Billyn Abdul: *_Typing📲_* *_SARAN ƁOYE!!_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_ƊANƊANO DAGA ZAFAFA BIYAR 2021_* No. 1 ...........Tun a farkon shigowa anguwar zaka shaida lallai ana biki, musamman da gidan da ake taron ya kasance shine na biyar a farkon shigowa layin.       Cike titin layin yake da yara da ƴammata harma da manya maza da mata. Musamman a cikin babban haraban massalacin dake manne da katafaran gidan da tun daga kallon gate ɗinsa zaka san ya wuce raini a gine da yalwar girma.       Rumfunane guda uku a tsaye, waɗanda gaba ɗayansu an cikasune da fararen kujeru bisa tsari. Rumfar farko cike take da manyan malamai masu faɗa aji a ƙasar dama wasu ƙasashen ƙetare musamman na musulmai. Rumfa ta biyu kuwa matane zalla a cikinta tundaga ƙanan har zuwa manya. Rumfa ta uku mazane suma manya da yara.       Babban abin birgewar da ƙayatarwar shine shigar kamala da mutunci dake tattare da jama'ar wajan. Duk da taron bikine kowa ya suturta jikinsa, babu wani mai shigar ALLAH wadai ta nuna tsiraicin da ake laɓewa da sunan biki.        Duk da cikar da wajen take da shi hakan bai hana yawaitar mutane a cikin gidanba shima. Lallai da gaske gidan babban gidane, dan a kallo ɗaya zaka fahimci gidan family house ne, dan kuwa yafi ƙarfin mallakar mutun guda kai tsaye. Daga jikin gate ɗin gidan zaka iya ganin dukkanin yawan ɓangarorin gidan da aƙalla zasu iya kai sashe biyar zuwa shidda, ginin iri ɗaya ne babu wani banbanci game kallo da ga nesa, saika shiga daga cikine ka fahimci kowa da kalar tsarin da yafi buƙata a nasa sashen.           Lokacine bana banbance minene a cikiba, ko mi aka tsara. dan haka nabi ayarin mutane masu kai kawo zuwa sashe na biyu da yafi ɗaukar jama'a. Kasancewar duk mutane na a harabar masallaci wajen da za'a gudanar da walima ya bani damar kutsa kai har cikin ɗakin da naji ana masa ishara da amarya na ciki.          Ƴammata ne da a ƙalla zasu kai goma zuwa sha a ciki, kowacce nata ƙoƙarin ƙimtsa jikinta dai-dai buƙatarta cikin doguwar riga milk color mai adon golden ɗin furanni da aka ƙawata da stones a gabanta da ƙarshen hannun. Hirarsu suke da dariya har baka iya jin mi wani yake faɗa.           “Oh ALLAH, Aure mai saka kowa hankali. Su o'e tunkan Yah Ab.. Yaci ƙaniyar bakin harya mutu haka?”. Ɗaya daga cikin ƴammatan dake naɗa ƙaramin golden veil a kanta ta faɗa tana ƙyalƙyalewa da dariya. Kusan a tare duk suka juya suna kallon wadda ke kwance saman gado ita kaɗai ta juya musu baya, kwance take rubda ciki da ɗaurin ƙirji sai ƙaramin hijjab a jikinta. “Hhhhh! Wlhy kuwa Iman, kinga dai bakin tsiwa tun jiya ya mutu”. Wata tabama mai maganar amsa tana dariya itama da ƙarasawa jikin gadon, yayinda suma sauran suke dariya suna nufar gadon. Sai da suka zagayeta sannan suka haɗa baki wajen faɗin “Gobe zata fashe!!!” tare da ƙyalƙyalewa da dariya suna tafawa.              Ƙaramin tsaki wadda ke zaune can gefen mirror tana kwalliya taja tare da taɓe baki, taɗan hararesu idanunta cike da ƙwalla, cike da fushi ta ajiye hodar da take shafawa ta fice daga ɗakin. Bama susan tanayiba, dan sukam hankalinsu nakan amarya suna cigaba da mata ihun “Gobe zata fashe!! Gobe zata fashe!!!”. Faɗi suke da ihu sosai suna dariyar tsokana irinta ƙawen da ƙuruciya ke ɗawainiya da su, dan gaba ɗaya yarane ƙanana da bazasu wuce 16-17 ba. Hawayen da tun ɗazun take haɗiyewa ne suka silalo saman kumatunta a hankali. Bata motsaba, kamar yanda bata buɗe ido ta kalli ƙawayen nata dake mata shaƙiyancin ba. Ita kaɗai tasan mi takeji a ranta tun daren jiya. Tabbas wannan ranace data daɗe tana fatan zuwanta itada masoyinta Yah Abdallah tun bata gama sanin ciwon kanta ba. Sai dai batasan miyasa tunda aka shiga satin bikin jikinta yay sanyi ba kuma. Tasan hakan bazai wuce nasaba da sabuwar rayuwar da zata wayi gari a cikinta gobe idan ALLAH ya kaimu ba. Ta sake matso hawayen masu zafi tana jan ajiyar zuciyar da har jijiyoyin wuyanta saida suka miƙe...........            “Ya salam! Yaran nan lafiyarku kuwa!!?”. Akafa faɗa a bayansu da ƴar kakkausar murya. Tsitt ɗakin yayi, duk suka juya suna kallon mai maganar. Ta sake tafa hann ayenta tana riƙe haɓa. “Oh ku ɗin nan, yanzu nan bama ku sakata ta shiryaba kuka zauna shiriritar da kukafi ƙwarewa akai?”.          “Afuwan Addah”. Ɗaya ta faɗa tana ɗan sosa bayan wuya na alamun jin kunya. Girgiza kai Addah tayi tana ƙarasowa gaban gadon, “To naji, ku fita ku bani waje na kimtsata”. Ɗai-ɗai suka ringa fita suna ƙananun ƙunƙunai na alamar ba haka sukaso ba, amma sanin yau Addah babu fuskar wasa tattare da ita yasa babu wanda ya iya cewa komai. Ita dai bata kulasuba, dan yau babu ƴan wasan a kanta. Kamo ƙyaƙyƙyawar budurwar tayi ta zaunar tana faɗin, “Tashi kinji dear, kukan ya isa haka, kefa amaryace, amaryarma mai tsada ga ƙyaƙyƙyawan miji irin Abdallah. Ko bakison auren a fasa ne?”.        Baki budurwar ta tura gaba tana sake matso hawayenta, sai kuma ta faɗa jikin Addah ta sake fashewa da kuka. Karan farko Addah tai dariya tana shafa bayanta. Tace, “Oh Rabbi, yau ga Nu'aymah shugabar tsiwar gidanmu tayi laushi darajar aure”. Ita dai sakema ƙarfin kukanta tai tana narkewa jikin Addah. Sunja kusan mintuna huɗu a haka kafin Addah ta ɗagota tana sake faɗaɗa fuskarta da murmushi, zaunar da ita tai sosai ta kama bakin mayafinta ta share mata hawayen fuskarta tas duk da wasu na silalowa kaɗan-kaɗan.          “Haba Nu'aymah'n Abbah kukan ya isa haka mana, ko an miki wani abune?”. Kanta ta girgiza tana sauke ajiyar zuciya a jajajjere. “To wani waje ke miki ciwo ne?”. Nanma ta girgiza mata kai. “Ikon ALLAH, to minene ya sakaki kuka irin haka? Keda zakiyi auren soyayya Nu'aymah?. Ki duba kowa a family ɗin nan cikin tsantsar farin ciki yake da auren nan naku, dangi ta ko ina sun iso gobe idan ALLAH ya kaimu kawai ake jira. Umm. Hajjo, su Abbanki damu baki ɗaya kowa yana cike da farin cikin wannan alkairi. Ɗazun nan mukai waya da Angon shima jirgin ƙarfe uku zasu biyo daga Abuja, yanzu hakama sun taso inaga shi da abokansa. Ai nazata yau ranar farin cikice a gareki mara misaltuwama Nu'aymah. Uhhmm?”.       Hannu tasa ta share hawayenta, cikin rawar murya tace, “Addah wlhy inajin tsoro ne?”. Da mamaki Addah tace, “Tsoro kuma Nu'aymah? To tsoro akan mi Uhhmm?. Ko wani abune ya faru dake bamu saniba?”. Nanma kanta ta girgiza mata tana haɗiyar zuciya dajan numfashi.        Addah ta sauke nishi tana girgiza kai, hannu ta ɗaura kan haɓarta ta ɗago fuskarta. “Kalleni Nu'aymah”. A hankali ta ɗago manyan idanunta da launinsu ya koma Jaa, gashi sun kumburo saboda kukan data sha ta saukesu akan Addah”. “Kukan ya isa haka kinji daughter, kicire komai a ranki babu abinda zai faru sai alkairi, duk wani tsoro da kikeji ki ciresa a zuciyarki, kiyi farinciki dan gobe ranarki ce idan ALLAH ya kaimu, fatanmu ALLAH ya sanya albarka a al'amarin ya baku zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba, ALLAH yasa wannan haɗi ya zamewa family ɗinmu alkairi duniya da lahira”.          A zuciyarta ta amsa da amin, a zahiri kuwa sai tai ƙasa da idanunta alamar jin nauyin ta. Lura da hakan yasa Addah yin murmushi da lakace dogon hacinta. Tace, “Yauwa tagaban goshin Hajjo tashi ki shirya gashi can har an fara walima babu amarya”.      Ɗan murmushin yaƙe kawai tayi da miƙewa bisa umarnin Addah. Dama tayi wanka tuni, dan haka ta sake wanko fuskarta yanzu kawai ta dawo inda Addah ke jiranta. Ƴar kwalliya taimata da bazata takurataba, kafin ta sata ta shirya cikin atanfa zani da riga pitch da ratsin Maroon. Ɗinkin yay mata ɗagwas ajiki kasancewarta mai murzajjen jiki, dan sam Nu'aymah ba siririya bace, badai za'a kirata mai ƙiba ba, amma jikinta a mulmule yake babu alamar rama sam duk da kasancewarta yarinya ƙarama sosai. Baƙar riga mai zubin alƙyabba da tasha ado da pitch zare aka bisa da stones ta saka mata, da ɗan turare kaɗan, ta bata flat takalmi baƙi ta saka wanda yayma farar ƙafarta data sha ƙunshi jaa da baƙi ɗas. “Masha ALLAH amaryan ɗana Abdallah” Addah ta faɗa tana mata alamar tayi ƙyau👌🏼 da hannu. Ɗan murmushi tayi da maida kanta ƙasa na alamar jin kunya. Yarinyar ɗazun dake jikin Window a laɓe tana kallonsu ta share hawayen da take faman yi tun ɗazun, duka maganar Addah da Nu'aymah akan kunnenta da idonta suka faru, ta taune leɓenta da ƙa rfi tamkar zata hudashi tana ƙoƙarin danne kukan dake neman kufce mata da ƙarfi...       Babu ɓata lokaci Addah ta taimaka ma Nu'aymah suka fito harabar gidan, inda sukaci karo da wasu tsoffin mata su kusan biyar. Da ɗan faɗa farar ciki ta watsa musu harara tana faɗin, “Wai mi kuke da amaryar a cikin gida da har yanzun an gaza kaita wajen walima Fauza?”. Cike da girmamawa Addah tace, “Ayi haƙuri Hajjo, mun tsaya shirine shiyyasa”.          “To wane shiri kuma nikam kamar wadda za'a kai ɗakin miji yau, kinga taho Zainabu”. Tai maganar da kama hannun amarya Nu'aymah. Babu musu Addah ta sakar mata ita tana murmushi da binsu da kallo har sai da suka isa gab da gate sannan ta sauke ajiyar zuciya. Yunƙurawa tai zata bi bayansu itama......... Caraf aka riƙe hannunta. Juyawa tai da sauri, sai dai ganin wadda ta riƙotan yasa taƙi cewa uffan. Kallon gefe da gefe tai, ganin mutane nata ɗan kai kawo yasa ta sake tsuke fuska tana kallonta....... “A'ah! Adawiya lafiya kuwa? Fauza mi akai mata haka?”. Firgigit Addah tai da ture hannun Adawiya daga kan nata tana harararta, sai kuma ta kalli mai maganar fuska a narke. “Umm bar wannan ƴar taki kinji, bansan mike damun kansuba daga ita har Nu'aymah, canfa na iskesu sun haɗe kai a ɗaki sunata dirzar kuka ko shiryawa basuyi ba, ni wannan shaƙuwa tasu har tsoro take bani wlhy, gashi kuma mai rabawa yazo....” ta ƙare maganar da sharce hawaye tana kallon Adawiya dake jikin Umm tana kuka tamkar ranta zai fita. Murmushi ƙyaƙyƙyawar matar mai tsananin kamanni da Amarya Nu'aymah tayi, ta sake rungume Adawiya a jikinta tana ƙoƙarin haɗiye nata hawayen da suka ciko mata idanu. “Ya isa kukan haka Daughter, kiyi haƙuri, namiki alƙawarin insha ALLAH duk yanda zanyi sai nayi dan kibi ƴar uwarki sai kuje can kuyi karatunku tare kamar yanda kuka fara a tare kafin ALLAH ya baki naki mijin kema musha biki”. Maimakon Adawiya tai murna sai ta sake fashewa da kuka tana ƙanƙame Umm. “Oh ALLAH, ya isa haka mana daughter, ko sokike muma ki sakamu kukan ne uhhhmm?”. Ɗagowa Adawiya tai zatai magana Addah tai saurin tarar numfashinta tana harararta ta ƙasan ido, “Faɗa mata dai Umm, tundama ance mata ga mafita an samu ba sai tai haƙuriba, nifa banason shashanci kuma, a haka zaki bama Nu'aymah ƙarfin gwiwar yin farin ciki? Haba mana, k........” “A'a Addah ya isa haka mana, a barta taji da abinda ya dameta dan ALLAH, ɗiyata muje ki shirya kinji, tarema zamu fita wajen walimar da anyi sallar la'asar”. Ɗan satar kallon Addah Adawiya tayi, ganin harar data watso mata ƙasa-ƙasa ya sakata saurin ɗagama Umm kai alamar to. Kamata Umm tai suka bar Addah a wajen, tabisu da kallo ƙasa-ƙasa tana ɗan murmushin jin daɗi...... “Uhhm Fauza! Dama ke naketa nema ashe kina anan”. Wata mata dake tunkarita ta faɗa. Juyawa tai da sauri ta kalli matar, sai kuma ta saki murmushi da faɗin, “Oh! Ya salam Yaya, wlhy namafa manta na barki kina jirana a kitchen, rigimar ƴaƴanki ta ɗaukemin hankali”. Ƴar dariya sukai a tare, tare da barin wajen suna cigaba da maganarsu. A waje kam dai har yanzu ba'a kai ga fara gudanar da komaiba, sai dai wata ɗaliba a cikin ƴammatan da zatai sa'anni da amaryace ke karatu cikin zazzaƙar muryarta, wanda hakan yasaka wajen yin tsitt ana saurarenta. Wasu zafafan motocine guda biyar suka shigo cikin layin, duk da mutane hakan bai hanasu kutso kaiba kansu tsaye jikin ƙofar babban gate ɗin harabar massallaci. a take mafi yawan mutanen dake a wajen walimar hankalinsu ya koma ga kallon motocin da sukai parking a jere abin birgewa. Kowa ya zuba ido yaga su wanene zasu fito a ciki?.... Ni kaina sai da na sauke numfashi da faɗin Masha ALLAH, saboda fitowar wasu samari masu ji da lokaci da gayu daga motar, da gani babu tambaya waɗanan abokan angone dama angon kansa, bankai ga cankar angonba wani mafi ƙyawun haiba da tsarin kwalliya a cikinsu ya fito a motar tsakkiya waya manne da kunnensa yana murmushi. Sanye yake cikin ɗanyar shadda Maroon color sai maiƙo take da ɗaukar idanu. Ya saki lallausan murmushi yana gyaɗa kansa alamar amsa mai maganar daga can, sai kuma ya sauke wayar ya tura aljihu dabin abokansa dake tsaitsaye suna kallon ƴan taron walimar da suma mafi yawansu su suke kallosu da kallo. Kafin yace wani abu ɗaya daga cikinsu ya juyo yana faɗin, “Woow Ab harfa na canko amaryarka”. Ɗan hararsa yayi da ɗauke kai kamar bazaice komaiba, sai kuma ya sake kallonsa yana wani furzar da numfashi. “Malamai dalla kallon ya isa haka, ku bakwa ganin su Baba Malam duk mu suke kallo suma”. A tare duk suka juyo da kallonsu garesa suna dariya, wanda yay magana ɗazunne ya sake faɗin, “Hahh! Go gefe malam, kai dai faɗa mana kishi kakeyi dan ance anga Angel ɗinka”. “Shashasha, to idan nayi kishin laifine?”. Abdallah ya faɗa yana ratsa tsakkiyarsu yay gaba. Cike da shaƙiyanci sukabi bayansa suna dariya ƙasa-ƙasa da faɗin, “Shege uban zumuɗi, anya kuwa zaka cika alƙawarin da kaima su Baba Malam na barin ƙwailarnan taka tai karatu? Karfa muji nanda wata tara ana nemanmu a labour room”. Duk da yana jinsu sarai bai tankaba, sai dai ya ƙawata fuskarsa da wani sassanyan murmushi daya ƙara fidda ƙyawun fuskarsa... “Huuhm Nu'aymah! Gafa Soulmate ɗinki nan tafe tamkar wani ɗawisu a tsakkiyar furanni”. Iman ta faɗa a hankali cikin kunnen Nu'aymah da kanta ke'a duƙe lulluɓe da abaya batasan wainar da ake toyawaba. Sassanyar ajiyar zuciya ta sauke da ɗan ɗagowa kaɗan, idanunta ne suka sauka akansa. Taja ajiyar zuciya tana lumshe idanunta wani sanyi na ratsa mata ƙirji. Sosai take tsananin son Yah Abdallah, kamar yanda tasan itama yana sonta fiyema da yanda take sonsa. Yah Ab farin cikinta ne, jinin jikinta ne, nutsuwarta ne, shiɗin na musamman ne a gareta, dan yana ɗauke da mataki uku ne na martaba a gareta. Shi ɗin jininta ne ɗan uwanta, sannan masoyinta tun batasan kantaba. Malaminta kuma na farko ta ɓangaren ilimi. Shiyyasa komai nasa abin girmamawane a gareta...... “Hy Baby! Kallon ya isa haka karki cinyesa mana”. Nanah ta faɗa tana ɗan mangare kan Nu'aymah. Karon farko da tunda aka wayi garin yau Nu'aymah tai murmushi har fararen haƙoranta suka bayyana, ɗan harar Nanah tayi da Iman da suke mata dariyar shaƙiyanci. Ta maida kanta ƙasa tana faɗin, “Sa'idiniyya kawai”. Nanma dariyar sukayi, ita kuma ta lumshe idanunta daga cikin hular abayar tana maijin nutsuwa da farin cikin isowar angonta lafiya bayan tsahon shekaru biyu kenan basuga junaba sai dai a waya da hoto da video call. Isowar ango Abdallah da abokansa tayi dai-dai da shigar lokacin sallar la'asar, dan haka aka sanar da zuwa ai salla. Mimmiƙewa mazan suka shigayi suna nufar bayan masallacin domin yin alwala, masu alwalar zuhur kuma da bata karyeba suna shigewa ciki. Matanma ba'a barsu a bayaba, wasu cikin gida sukaita shiga, wasu kuma sama inda massallacin mata yake. ★★★★★ Baƙi da suka janyema Umm hankali ya saka Adawiya samun damar silalewa ta nufi ɓangarensu. Nan ɗinma akwai mutane babu laifi, musamman da a yanzu aketa shigowa domin gabatar da sallar la'asar. Sashen Abbansu ta shige, inda ta tabbatar bazata samu kowaba sai su ƴan gida. Ilai kuwa babu kowa sai ƙamshi dake ta tashi mai daɗi. Ɗakin farko dake a falon sashen ta buɗe ta shiga, babbane yasha kayan more rayuwa tsaf, ta zube a saman gadon tana sauke wata nannauyar ajiyar zuciya mai tafiya da kuka mai ƙarfi da hasala zuciya....... Turus Addah data fito daga bayin ɗakin fuskarta jiƙe da ruwa alamar tayo alwalar yin salla tayi a bakin ƙofa tana kallonta, a take idanunta suka rine da ɓacin rai, cikin faɗa tace, “Wai wane kalar shashancine wannan kikema mutane haka Adawiya?!!”. Adawiya da sai yanzu tasan da shigowarta ta taso da gudu ta faɗa jikinta da sake fashewa da wani sabon kukan, “Addah Wlhy ina sonshi, idan baku auramin shiba mutuwa zanyi, wlhy saina kashe kaina Addah. Dan nafita sonshi ku taimakeni.............” Ta fashe da wani irin kuka tana zamewa zata faɗi ƙasa jikinta na rawa. Da wani irin kallo Addah ta bita harta zube ƙasan yaraf, taɗanja jikinta baya tana jan tsaki zata raɓata ta wuce. Saurin tashi Adawiya tai zaune ta riƙo hannunta. “Wlhy Addah inhar baku aura masa ni ba saina kasheta!!”. Baya Addah tai da sauri zata faɗi ƙasa tana mai waro idanu waje sosai akan Adawiya, bakinta na ɓari tace, “Ki kasheta Adawiya?!”. “Da hannun nan nawa kuwa”. Adawiya ta faɗa tana zazzaro idanu waje itama da ɗaga hannunta tana nunama Addah............✍ Hummmmm!!!! Turƙashi. Masu karatu wannanfa shine ana dara sai ga dare yayi😲. Mi kuke tunani akan wannan labari? Wacece Adawiya? Sannan wacece Nu'aymah? Wanene Kuma Abdallah?. yaya zata kasance? Minene zai faru kuma? Wace amsa Addah zata bama Adawiya?...... Amsar waɗanan tambayoyin duk suna a Littafin SARAN ƁOYE!! da ke cikin tawagar littatafai biyar na zafafa 2021 dake shirin zuwa muku insha ALLAHU nan bada jimawa ba😉😋. Wlhy karku bari ayi babuku, dan ZAFAFA BIYAR 2021 fa da zafinsu suke tafe, na tabbatar muku tafiyar wannan shekarar ta dabance MASOYAN AMANA😋🤗🤗😀😀. ZAFAFA BIYAR 2021 Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......! (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗 Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗 Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗 Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗 Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋 Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇 09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* *_SARAN ƁOYE!!_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* Free page😋 No. 2 .................Tsaki Addah taja tana ballama Adawiya harara, ta tsallaketa ta wuce tana faɗin, “Sai kije ki kashetan shashasha kawai mara tunani”.          Kuka sosai Adawiya ta sake fashewa da shi. Ta rarrafa har inda Addah take shirin kabbara salla ta riƙe mata ƙafafu. Cikin fushi Addah ta ƙwace ƙafafunta tana nuna Adawiya, “Wlhy idan baki shiga hankalinkiba Adawiya zan bala'in saɓa miki, wai wane irin iskancine wannan? Ki shiga hankalinkifa tunkan nai miki abinda zakiyi dana sani a taron bikin nan. Dalla tashi ki ficemin anan, ba kashe Nu'aymah ba ki babbakama gidan wutama mu ƙone ƙarewar hauka. Wawuya kawai!!”.           Yanda Adawiya taga ran Addah ya ɓaci tasan zata iya cin ubanta kamar yanda ta faɗa, tana ganin ta kabbara salla saita tashi ta fita tana kukanta. Addah mace ce mai yawan wasa da fara'a, idan har kaga fushinta to lallai an kaita maƙura, shiyyasa idan tai fushin dolene kaji shakkarta. Su kansu ƴaƴanta tana rayuwa da sune tamkar ƙawayenta, hakama sauran yaran gidan. Wannan halayar tata tajan yaran a jiki yasa kowane yaro yazama ɗan ɗakin Addah a gidan, suna sonta sosai, hakama iyayensu sunajin daɗin yanda take son ƴaƴansu da basu lokacinta.                    Can bayan ɗakunan sashen samarin gidan Adawiya ta nufa, dan tasan canne kawai babu mutane. Waje ta samu ta zauna tasha kukanta, yayinda zuciyarta ke shirya mata mugayen abubuwa game da Nu'aymah da matakin da zata ɗauka a kanta na dakatar da wannan auren, tayi alƙawarin kota halin ƙaƙa saita mallaki Abdallah a safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu. Sai kuma ta rabashi da Nu'aymah, idan kuma har hakan bata tabbata ba to sai dai suyi zaman kishi ita da Nu'aymah kokuma kowa ya rasa. Dan ko sama da ƙasa zata haɗe bazata barma Nu'aymah Abdallah ba wlhy........         “Adawiya! Adawiya!!”. ta jiyo ana ƙwala mata kira. Tsaki taja mai ƙarfi kafin ta miƙe tana kakkaɓe jikinta daya ɗan ɓaci da ƙasa, duk da ma ita ko shiryawa batayiba. Fitowa tai inda zata iya ganin mai kiran nata. Da sauri taja baya saboda karo da suka kusa ci da Yah Abdallah. Ƙirjinta yay wani mugun harbawa, a take ta fara neman nutsuwarta ta rasa. Kwarjininsa da matsanancin son da take masa suna neman birkitata gaba ɗaya ta kasa riƙe kanta....          Sassanyan Murmushinsa ya sakar mata yana ɗan ware idanunsa a kanta, “Oh Hassanar amaryace haka bata ko shiryaba?”. Duk da maganarsa batai mata daɗiba saita saki masa murmushi, ta matsa kusa da shi tana shaƙar ƙamshin turarensa mai daɗi, “Yah Abdallah dama ka iso?”.        “Ya za'ayi ki sani tunda ance kina nan kinata kukan rabuwa da Husainar ki”. Baki ta buɗe zatai magana sai kuma ta fasa tana kallon Amal data rako Yah Abdallahn. “Kiranmi kike ƙwalamin ke kuma?”. Baki Amal taɗan taɓe tana cigaba da latsa wayar hannunta, “Kiranmi zan miki ni kuwa, dama Yah Abdallah ne ke nemanki, shine akace anga kinyo tanan”.       Kafin tace wani abu Yah Abdallah yace, “Nine na sakata, wani aiki zakimin, Amal jeki abinki”. Kai Amal ta jinjina masa, tai gaba abinta batare data sake kallon inda Adawiya take ba. Sai da tai nisa da su sannan Abdallah ya sake kallon Adawiya, ganin shi take kallo sai yay murmushi.        “Yaya dai ƙawar amarya na canja miki ne?”. “Sosaima kuwa Yah Abdallah”. Adawiya ta faɗa cike da yanga tamkar ba itace ta gama darzar kukaba yanzun.       Murmushi yayi yana ɗauke kansa da faɗin, “To na gode. Kinsan aikin da zakimin?”. Kai ta girgiza masa batare da tace komaiba. “Sonake kije wajen Walimarcan ki satomin amaryata nan inason ganinta”. Wani takaicine ya soki zuciyar Adawiya har fuskarta sai da ta nuna hakan. Da mamaki Abdallah yace, “Yaya dai?”. “Babu komai Yah Abdallah” ta bashi amsa da rawar murya.           “Okay, to maza ki shirya saiki ɗakko min ita, karfa ki bari kowa ya ganki musamman ma Hajjo”. Kanta ta ɗaga masa kawai, dan tasan idan tai magana kukane zai ƙwace mata. Da kallo Abdallah ya bita harta ɓacema idanunsa, haka kawai tausayin yaran ya kamashi, kowa yasan irin shaƙuwar dake tsakanin Adawiya da Nu'aymah tun ƙuruciya, sun tasone tamkar tagwaye a gidan, komai tare ake musu shi, yanzu kam ace zasu rabu rana tsaka ai dolene kaji tausayinsu.         Adawiya kam koda ta bar wajen sashen Hajjo kakarsu ta nufa, babu kowa duk ana wajen walima, dan ana idar da salla kowa ya koma, daga cikin gidanma kana jiyo lecture ɗin da aka fara. Kwanciyarta tayi dan ta rantse bazata kira Nu'aymah ba. ★★★         Tun Abdallah na kallon hanya na jiran ɓullowar amaryarsa Nu'aymah da Adawiya harya koma duban agogo. Kamar wasa sai ga mintuna ashirin sun shuɗe babu Adawiya balle Nu'aymah, abinda zuciyarsa kawai ta basa Hajjo ta hana Adawiya ɗakko Nu'aymah ne, maybe kuma tanacan tana wayon yanda zasu baro wajen. Ɗan murmushi yayi yana lumshe ido, sosai yake cike da ɗoki da ƙaguwar son ganin Nu'aymahr sa, yanason yaga yanda ta sake komawa yanzun........          Kiran da ake masa a wayane ya katse tunaninsa, ya zaro wayar daga aljihun gaban rigarsa ya duba. Zaid ne, kamar bazai ɗagaba sai kuma ya amsa tare da ɗorawa a kunnensa. “Hello Jibiya wai kana inane?”. Kamar bazaice komaiba sai kuma yay guntun tsaki da kallon agogon hannunsa. “Ina cikin gida mana, miya faru?”. “Cikin gida kuma? To mi kakeyi acan bayan kowa duk yana nan har amarya. Gashi nan Baba malam na nemanka to”. Baice masa komaiba ya yanke wayar. Badan yaso ba ya baro cikin gidan ya koma wajen walimar.          Inda Nu'aymah ke zaune kusa kakarsu Hajjo ya kalla, tana zaune a yanda ya barta tun ɗazun, babu kuma alamar Adawiya a wajenma. Ɗan tsaki yayi a ransa ya ƙarasa inda Baba Malam yake.              Masha ALLAH, anyi taron walima an tashi lafiya, inda malamai suka ragargaza lectures masu ratsa jiki ga ma'abocin saurare. Gaba ɗaya an gina sune akan zaman aure da kurakuran da muke tafkawa a cikinsa da hanyoyin magancesu, inda amarya da angonta sukasha addu'oin fatan alkairi da zaman lafiya. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________ Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 ____________________________         Tunda aka tashi jikin Nu'aymah sai ya sake yin sanyi, maimakon ta nufi ɗakinsu da suke zaune da ƙawayenta sai ta nufi wajen Umm. Kanta tsaye ɗakin Umm ta wuce, sai dai bata ciki sai ƴan uwanta. Gaishesu tayi suna tsokanarta da amarya-amarya, ita dai kanta a ƙasa ta sulale ta fito. Sashen baba malan ta nufa, dan tasan Umm bazata wuce tana a canba ko wajen Addah.             Tun shigowarta corridor ɗin daya shiga tsakanin falon Baba malam dana Umm taga takalman Umm da Addah, ɗan murmushi tayi tana sake jinjina wannan irin ƙauna ta iyayensu, ƙofar falon ta ƙarasa tare dayin sallama, daga ciki suka amsa mata da bata iznin shiga.        “Ah ah! amarya da kanta. Miya farune?”. Addah ta faɗa tana murmushi. Kallon Umm da batace komaiba Nu'aymah tayi, sai kuma ta duƙar da kanta hawaye na cika mata ido. Addah tace, “Kinga zonan”. Takawa tai a hankali zuwa garesu, ta zauna a ƙasa jikin ƙafafun Umm data cigaba da abinda takeyi tamkar batasan da shigowar Nu'aymah ba.         “Ƴar albarka miya farune? Ko kewar Umm ne ya motsa?”. Maimakon Nu'aymah ta bama Addah amsar tambayarta sai hawaye suka gangaro mata a kumatu, ta kwantar da kanta bisa cinyar Umm tana jan ajiyar zuciya a jajjere.       Dauriya kawai Umm keyi dama, taja ɓoyayyen ajiyar zuciya da girgiza kanta tana kallon Nu'aymahn. “Ke kuma wannan shashancin fa?......”       “A'a babu wani shashanci Umm”. Addah ta faɗa tana kamo hannun Nu'aymah cikin nata. “Baby faɗamin miya faru? Ko har yanzu tsoron dai?”. Kai Nu'aymah ta ɗaga mata, sai kuma ta ɗago ta kalli Umm da itama kallonsu takeyi. “Umm dan ALLAH ni banason auren a fasa kawai”.          “Afasa kuma Nu'aymah?! Miyasa?”.        “Addah wlhy ni naji banaso yanzun kawai”.         Sosai abin ya bama Addah dariya, ita kanta Umm sai da tai murmushi tana girgiza kai, dan babu komai a maganar Nu'aymah sai zallar ƙuruciya da sakarci. Umm ta janyeta a jikinta tana miƙewa da faɗin, “Wannan shashancin ba daniba, Addah bara nayi nan kinji”.       Sauri riƙeta Nu'aymah tayi tare da sake cukuykuye ƙafafunta tana kukanta, “ALLAH Umm nidai banaso, gara na zauna a wajenku Please”.        “Oh ALLAH, Nu'aymah banason sakarci kinji, sakarni naje nayi abinda zai amfaneni”.           Kallon Umm Addah tayi, cikin magana da yaren ido taima Umm alamar ta lallasheta Please. Umm zatai magana Addah ta girgiza mata kai tana miƙewa ta fice ta barsu. Ajiyar zuciya Umm ta sake saukewa a sanyaye, kafin tai guntun murmushi da komawa ta zauna a inda ta tashi. Kama Nu'aymah tai ta tadata ta maidota kan kujerar kusa da ita ta zaunar. Hakan ya bama Nu'aymah damar faɗawa jikin Umm ta rungumeta.          Karan farko Umm tai ƴar dariyar ƙarfin hali da rungume ɗiyar tata itama. “Ke wai bakisan kin girmaba Nu'aymah? Aurefa za'a ɗaura miki gobe idan ALLAH ya kaimu amma kike halin yara har yanzun?”.         “Umm ni wlhy na fasa, zan zauna a wajenku nayi karatun kawai”. Dariya Umm ta sakeyi da ɗago fuskar Nu'aymah ta share mata hawayenta. “To naji ya isa haka nan kukan ko”. “To Umm za'a fasa ɗin?”. “Tambayi Abbanki ga shinan”. Umm ta faɗa tana kallon Abba daya shigo kusan mintina biyu kenan harya zauna kusa da Nu'aymahn bata saniba yana kallonsu kawai. Tashi Nu'aymah tayi daga jikin Umm takoma jikin Abbanta.          “Maman nan nawa dai shagwaɓanta yayi yawa”. Ya faɗa fuskarsa ɗauke da murmushi yana shafa kanta. Ɗagota yayi ya zaunar sosai, tare da saka hannu ya share mata hawayenta gaba ɗaya. “Kinga faɗamin miya faru?”.          “Abbah a fasa kawai”.     Waro idanu ya ɗanyi cikin mamaki, “Mamana mi za'a fasa?”. “Abbah aur.....” sai kuma ta kasa ƙarasawa tai ƙasa da kanta.           “Ina jinki faɗamin mana!”. “A...Abbah auren, ni yanzu na fasa”.            Kallon juna sukai shi da Umm dake kallon Nu'aymah cike da damuwa, Sosai ta basu tausayi da dariya, amma duk sai suka danne kayansu. Abbah ya riƙe hannayenta da sukasha ƙunshi cikin nasa, cikin muryar lallashi yace, “Mamana kin daina son yayan nakine?”. “A'a Abbah”. Ta faɗa kanta a ƙasa. “To miyasa kikeson a fasa?”. “Abbah banason rabuwa daku nidai”.          Murmushi Abbah yayi tare da sauke ajiyar zuciya, “To ai ba rabuwa zakiyi damuba Nu'aymah, kuma shima Abdallah ai ɗan uwankine mai gatantaki ma fiye da kowa a gidan nan, duk kuma sanda kikeso ya kawoki wajenmu zai kawoki”. Idanunta cike da kwalla ta kalli Abbah, “To Abbah ina zai samu kuɗin jirgi yayta kawoni kullum tun daga Saudia?”. “To ai dama ba kullum ba Mamana, keda zakiyi karatu tayaya za'ace za'a kawoki gida kullum koda anan zaku zauna ma. Duk dai sanda kuka sami hutu sai ya kawoki, kuma muma zamu dinga zuwa ganinku ai ko”. Shiru tai batace komaiba, sai hawaye keta sake mata zarya.        Cikin hikima da wayo Abbah da Umm sukaita mata nasiha da ƙara ƙarfafa mata gwiwa harta daina kuka ta koma dariya kamar ba ita ba, kusan awarta ɗaya da rabi a wajensu sannan ta tafi kiran da hajjo ta aiko Farida tai mata.               Tafiya take tana ƙunƙunin haushin Hajjo, dan tasan kiran datai mata bai wuci sakata shiga cikin ruwan lalle ba, itako ta tsani abun dan ƙyanƙyami takeyi, amma jarabar kakar tasu bazai bari ta fito ta faɗa ba.          Gabanta ne ya faɗi jin an kamo hannunta, ta juyo a firgice zata wage baki tai ihu aka rufe bakin.       Cikin muryarsa mai sanyi da nutsuwa yace, “Matsoraciya nine. Na gaji da wasan ɓuyar da kikeyi dani malama”.       Ajiyar zuciya Nu'aymah ta sauke jin Yah Abdallah ne, ya saketa yana cigaba da ƙawata fuskarsa da murmushi da ƙare mata kallo daga sama har ƙasa. “Saboda kinsan kin sake haɗuwa fiye da da shiyyasa kiketa faman ɓoyemin kanki ko?”.        Hannu Nu'aymah tasa ta rufe fuskarta da shi tana murmushi, “Yah Ab banfa san kazo ba”.         “Kutt!”. Ya faɗa yana zaro idanu waje, “Wato bama kisan nazoba?”. Kai ta jinjina masa da ƙyalƙyalewa da dariya.           “Lallai yarinya na yarda kin girma kam, idan ba tsoroba buɗe fuskar ki faɗamin ido da ido mana”. “A'a ai basai na buɗeba tunda dai kaji na farko”. “Hahyh! Zaki min bayani gobe idan ALLAH ya kaimu ai”.         Kasa cemasa komai tai a kan hakan, saima ta risina kawai ta gaidashi. Ya amsa mata cike da kulawa idanunsa na cigaba da yawo a jikinta, duk da akwai ƙaramin hijjabi tare da ita, rayawa kawai yake a ransa ‘anya baiyi gangancin ɗaukar alwashin rinon Nu'aymah ba kuwa? Kai da sakel wai anbama mai kaza kai’.......           “Yah Ab bara naje hajjo ke kirana”.      Maganarta ta dawo dashi hayyacinsa. Ajiyar zuciya ya sauke daɗan kallon gefensu, sai kuma ya kalleta sosai yana gyara tsaiwarsa. “Babie kinga manta da tsohuwar can kinji, musamu guri mu zauna muɗan zanta na yaushe gamo, ke koma ɗokin ganina baƙyayi bayan kuma shekara biyu kenan baki ko ganniba”.           Murmushi tayi tana ɗan kallonsa ta gefen ido, a ranta godiya takema ALLAH daya mallaka mata Yah Ab matsayin masoyi, gobe idan ALLAH ya kaimu kuma iyanzu mijine. Ya haɗa abubuwa masu yawa na gwaranzan mazaje da kowacce mace zatai alfahari da samunsa, ita kanta tasan ta cika mai sa'a ta gaske, dan ba'a wajeba ko'a cikin yayyenta, ƴan uwanta tasan akwai masu tsananin sonsa, amma ya dage kai da fata sai ita, tun batasan kantaba, tun ana masa faɗan yay aure idan ta girma sai ya ƙara da ita har kowa ya zuba masa ido dan yaƙi amincewa, a cewarsa ita kaɗai ta ishesa rayuwa, dan haka zai jirata ko tsahon shekara nawane. Damuwa da rashin auren nasa ya saka iyayensu yanke hukuncin aura masa ita bayan sun kammala secondary wata uku kenan, acewarsu taje ta cigaba da karatun a ɗakinsa kawai..........            “Ina kika tafi kika barni Noor?”. Ya faɗa yana kaɗa mata hannunsa saitin fuskarta. Ajiyar zuciya ta sauke da duƙar da kanta tana murmushi. “Muje” ya sake faɗa yana nuna mata hanya.       Babu musu ta bisa zuwa can bayan sashen Hajjo, inda kuma ya kasance gaban sashen Abbansu Musbahu. Zama sukai a fararen kujeru dake a wajen, basufi mintuna uku da zamanba sai ga Adawiya. Sosai Nu'aymah taji daɗin zuwan ƴar uwar tata, dan dama a takure take da kasancewarsu su biyu kawai ita da Yah Abdallah. Shiko sam baiso hakanba, amma sai bai nunaba ya biye musu sukaita zuba masa shirmen surutunsu.        Ganin hirar dai bazata yuwu shida Nu'aymah kawai ba sai ya miƙe bayan kamar mintuna 35 da zamansu, umarni ya basu suje su kwanta, shima zai koma wajen abokansa suna jiransa. Sam Adawiya bataso hakaba, dan wani irin farin ciki ta tsinta kanta a ciki na kasancewa da Yah Abdallah a ƙarƙashin inuwa ɗaya. Sai da yaga sunbar wajen sannan shima ya miƙe ransa duk babu daɗi, dan yaso su tattauna abubuwa masu muhimmanci shi da Nu'aymah amma Adawiya tazo ta tsare ko ina.            Ɗakinsu dake a sashen su Nu'aymah suka nufa, inda ƙawayensu suke. Wasu sunyi barci, wasu ko na hira a waya da samarinsu, wasu kuma cheating, ƙalilanne ke hira a tsakaninsu.         Yusrah data fito daga bayi tace,  “Aymah wai ina kika shiga Hajjo nata nemanki? Sai masifa takeyi tun ɗazun, dan tazo ɗakin nan yafi sau goma”.             “Yah ilahi, dan ALLAH da gaske Yusrah?”. “Wlhy karkiji wasa, tambayi su Nanah ma kiji, har Addah ma sai da tazo nemanki. Ina kikaje to ke?”.             “Muna tare da Yah Ab ne fa da Adawiya”.    “Ohhh! Kice soyayya ce ta lula dake sama. Aiko daga ke har Yah Ab ɗin kunga banu da jaraban Hajjo da safe idan ALLAH ya kaimu, ga ruwan turare can Addah tace idan kin dawo ki shiga ciki”.          A sanyaye ta amsa da “to”, sauran kuma suka sanya mata dariyar tsokana.       Bata kulasuba ta nufi toilet ɗin, Adawiya kuma taja tsaki ta fice daga ɗakin batare dasu sunma lura da itaba. _______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 __________________________          Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 Muna godiya da zaɓin zafafa biyar😍😘👌🏼🤗 ________________________________          Har Nu'aymah ta cire kaya zata shiga bahon da Addah ke haɗa mata ruwan turare saita tuna da tabar wayarta a sashen Abbah, gashi Yah Ab yace mata zasuyi magana ta Cat. Towel ɗin wankanta babba ta cira daga ƴar durowar da suke sakawa, ta ɗaura sannan ta fito ɗakin ta ɗauki babban hijjabi dogo ta zumbula. Batace ma kowa komaiba ta fice daga ɗakin zuwa sashen Abbah.        Sai da tai sallama a ƙofar ɗakin aka bata iznin shiga sannan ta shiga, Abbah ta iske shi da Abban Abuja suna shan shayi, ta gaida Abban Abuja kanta a ƙasa dan haka kawai yau kunyarsa takeji fiye da kullum shi Da Mamah. Shikam fuskarsa ɗauke da murmushi yake kallonta, “Mamana ai tun ɗazun nake baza idon ta ina zan ganki amma kin ɓoyemin gaba ɗaya”..         “Lah Abba ba ɓoyewa nayiba, ALLAH bammasan ka iso ba”. Ƴar dariya yayi irin ta kamilan mutane, yace, “To shikenan na amince mamana, kina lafiya ko?”. “Eh Abba lafiya lau”. “To Alhmdllh Mamanmu”.       Juyawa tai batare da tayi zancen wayarba, dan da anan ta barta tasan Abbah zaiyi magana. Tunanin zuwa inda suka zauna da Yah Ab tayi danta duba ko acan ta yadda bata saniba.          Gidan yayi shiru, dan mafi yawan mutane ƴan biki sunyi barci kasancewar har 12 ta gota, sai ɗai-ɗaiku marasa barcin wuri. Duddubawa ta farayi kasancewar akwai wutar Gen da aka tada, kamar wasa saita jiyo ring ɗin wayar acan gaba da inda take. Cikin mamaki da kila wakala ta nufi inda takejin, sai dai a ranta tana son ƙin gaskata wayartace, tafi tunanin wanine mai irinsa dai.      Tana tafiya Ring ɗin wayar na sake gaba, da kuma ya yanke zataji an sake kira, saita fara tunanin ko Yah Ab ne keta jera mata kiran? Ƙila ya hau online bai gantaba. To amma miyasa kamar ana tafiya da wayarne?. Babu mai bata amasa, ƙuruciyarta baisa ta fahimtar da ita akwai matsalaba kuma ta cigaba da bin sautin ring ɗin wayar har ta iso ƙaramar ƙofar da akai daga cikin gidan ta ɓulla massallacin ƙofar gidansu, inda su Abbah kebi da asuba yin sallar asuba dasu ma kansu idan suna buƙata ko zasu shiga islamiyya.        Anan ne ta tsaya cak tana waige-waige. Sai kawai taji an jeho mata abu akan fuska. Saurin saka hannu tayi ta janye guntun handkerchief ɗin da aka jeho mata fari tas. Kafin ta samu damar yin wani tunani akan hakan ko neman taimako taji duk jikinta ya saki idanunta na wani lumshewa kamar wadda hankalinta ke neman gushewa daga gareta.       Daga haka bata sake sanin mike faruwaba kuma...............✍ Tashin hankali, to wanene kuma ya da wannan aiki😲🤦🏻🚶🏻?. Amsarku na a Littafin SARAN ƁOYE dake cikin rukunin littatafai biyar na ZAFAFA 2021 da a yanzu haka sun fara zuwa muku da ɗumi-ɗuminsu, karku bari a baku labari guys, wannan tafiyar tanada banbanci sosai dana baya ina ƙara tabbatar muku😉👌🏼😀😍😍😘💃🏻😋.            ZAFAFA BIYAR 2021 Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* *_SARAN ƁOYE!!_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* Free page😋. No. 3 ...............Sama-sama takejin motsin mutane na matsota, sai dai bata fahimtar maganar da sukeyi balle ta ɗauki muryar kowa. Ta dafe kanta dake tsananin juya mata tare da jingina jikinta da bangon daya raba gidan nasu da massallaci. A hakanma dai bata tsiraba, garin cigaba da mata hajijiya yakeyi. Tai ƙasa zata zame ta faɗi aka riƙota. Ƙoƙarin buɗe ido take taga wanene? amma ta kasa saboda nauyin da sukai mata, haka ta sake jiki ga koma wanene ya riƙeta sosai, kafin ya fara janta suna takawa a tare batare da tasan ina suka dosa ba.           Tabbas taji an sakata a mota an kwantar, amma daga haka bata sake sanin komai dake faruwaba a duniyar, dan barci mai nauyin gaske yayi awan gaba da ita....... ★★             A ɓangaren Abdallah kam yata jiran Nu'aymah ta buɗe data amma sai yaji shiru, sai kusan 12 yaga tazo online ɗin, yay mata magana sai dai ta buɗe saƙon amma bata amsashi ba. Hakan yaso sosa ransa, amma kuma daya tuna ƙuruciya na bala'in ɗawainiya da Nu'aymah sai ya watsar da abin yay kwanciyarsa, a cewarsa ai daga dai gone idan ALLAH ya kaimu duk wani zagaye-zagaye ya ƙare kuma, tunda ta zama tasa. Da wannan tunanin yay barcinsa batare da ya sake bi takan wayarba ma. ______________________________               A firgice ta farka jikinta jiƙe sharkaf da gumi. Baba malam dake saman abin salla ya kalleta da mamaki, sai kuma ya ajiye Al-Qur'anin hannunsa ya miƙe zuwa gareta. Zama yay kusa da ita ya rungumeta dan ya kula sam bata cikin hayyacinta, da alama kuma wani mafarkin tayi mara daɗi. Sai da sukaja kusan mintuna huɗu a haka ya tabbatar numfashinta ya dawo dai-dai sannan ya ɗagota ya bata ruwa ta sha. Sai da tasha kamar rabi ta miƙa masa sauran tana sauke ajiyar zuciya. “Jannat! lafiya kuwa?”. Ya faɗa yana share mata gumin goshinta.         Umm taɗan dafe kanta tana kallon mijin nata, “Abban Nu'aymah mafarki nayi wlhy, kuma akan Nu'aymah ne. Inaga bara naje na dubata a ɗakinsu” tai maganar tana ƙoƙarin sauka ƙasa.      Saurin riƙota yay da faɗin, “Ah ah Jannat”. Kallonsa tai tamkar zata fasa kuka, muryarta a sanyaye tace, “Inaji a jikina Nu'aymah tana cikin damuwa  Abbansu”. Murmushi yayi daɗan girgiza kansa. ya kamata ya maida ya kwantar tare da duƙawa ya sumbaci goshinta. “Nasan maganganunta na ɗazun da kika saka a ranki yasa kikejin kamar bata da lafiya, ki kwantar da hankalinki Jannat, ƙuruciyace kawai ke ɗawainiya da Nu'aymah, idan bamu ƙarfafata ba karmu yarda taga gazawarmu muma, kiyi haƙuri kimata addu'a kinji”.       Kanta ta ɗaga masa tana haɗiye kukan da ya cika mata idanu, sai kuma tai ɗan murmushi domin ƙoƙarin danne abinda ke azalzalar ranta har yanzun. Kanta ya cigaba da shafawa a hankali da tofa mata addu'a har barci ya sake kwasheta. Ya sauke numfashi a hankali da sake sumbatar goshinta sannan ya miƙe ya koma inda yake da.     ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 ____________________________       WASHE GARI    Tun kiran sallar farko wasu daga jama'ar gidan da makusantansu suka tashi aka fara ƙaƙainiyar ɗaura abinci. Hajjo data kwana da haushin Nu'aymah da batazo kirantaba ta nufi sashensu Nu'aymahn tana faɗa akan yau sai taci ƙaniyarta duk da ranar aurenta ce.          Masu kai kawon fita can waje inda aka ɗaura girki sunata gaisheta, amma amsawa take sama-sam dan a ƙule take, tana nufar ɗakinsu Nu'aymah. Babu wanda ya tashi a cikinsu, dan mafi yawansu basuyi barici da wuriba, Hajjo ta kunna fitilar ɗakin tana kiran sunan Nu'aymah. “K Zainabu! Zainabu kina inane wai?”.         Amal ce ta fara farkawa saboda bata da nauyin barci sam, ta tashi zaune da ƙyar tana murje idanunta da faɗin, “Kai Hajjo! Kinzo mu kin tadamu da kwakwazonki wlhy”. “Ubanki Lurwanu ne ke kwakazo, mara kunyar banza”. Tura baki Amal tai tana komawa ta kwanta dan taji haushi Hajjo ta faɗi sunan Abbansu.        “K ni tashi dan gidanku ki faɗamin ina Zainabu take?”.       “Ba tana sashenki ba” Amal ta faɗa tana juya ma Hajjo Baya. “K Safiya banson lalata, dan gidanku tana sashena zanzo nan nemanta ne?”.         “ALLAH Hajjo tana sashenki, bayan ta dawo muka faɗa mata kina nemanta shine ta tafi can”. Nanah data tashi yanzu itama ta faɗa cikin muryar barci.       Hajjo tace, “To sai dai idan tana ɗakin uwarta ko kuma wajen Fauza. Dan nidai ban gantaba, Adawiya ce kawai ta kwana a ɗakina”. Nanah tace, “To sai dai idan tana sashen Addah, dan ɗakin Umm su Mom ne suka kwana, nasan kuma Nu'aymah bazataje cikinsu ta kwanta ba Hajjo”.        “To bara na dubata wajen Fauzan, kuma saiku tashi kuyi salla tunda lokaci yayi”. “To” kawai Nanah tace. Amal kuwa bata sake maganaba har Hajjo ta fita.        Hajjo na fita Umm na shigowa, tadasu ta shiga yi dan su Nanah ma komawa sukai suka kwanta ganin Hajjo ta fita. Sai raba idanu Umm keyi a tsakaninsu nason ganin Nu'aymah, sai dai sam babu ita a cikinsu. Kafin ta samu damar tambaya Hajjo ta sake shigowa Addah biye da ita a baya.        Cikin girmamawa Umm ta rissina tana gaida Hajjo. A taƙaice ta amsa mata da tambayarta ko Nu'aymah a ɗakinta ta kwana ne?. Gaban Umm yay masifar faɗuwa, ta girgiza kanta da haɗiye yawu da ƙyar. “A'a Hajjo ba can ta kwanaba”.        “Yau mun shiga uku”. Cewar Addah tana ida shigowa ɗakin sosai. “Ku batare kuka kwana da Nu'aymahr ba ne wai?”.         Yusrah tace, “A'a Addah, batare muka kwana da itaba, bayan kin haɗa mata ruwan turare kin fita suka shigo ita da Adawiya, to na faɗa mata dai ga ruwa can kin haɗa mata ta shiga ta amsa da to. Sai dai tana shiga bata jimaba ta fito ta fice daga nan, ni dai har barci ya ɗaukeni bata dawo ba, kuma kusan nice ƙarshen barci”.          Tashin hankaline ƙarara ya bayyana a fuskar Umm dasu Addah, basu tsaya jan zancenba suka fito daga ɗakin domin neman Nu'aymah a sauran sassan gidan ko taje wani ɓangaren ta kwana.           Ɓangaren Momy mahaifiyar Abdallah suka fara shiga tace rabonta da Nu'aymah tun a wajen Walima, amma bara a duba kotazo ta shiga ɗakin su Amal bata saniba. Sun duba ɗakinsu Amal babu kowa sai ƙannen Amal ɗin biyu dake barci. Sauran ɗakunan kuma duk akwai baƙi da wahala ace ta shiga can, amma duk da haka sai da suka shishshiga suma. Amma babu ko mai alamarta.      Sun koma sashen Abba Musbahu nanma dai matarsa Ammi da Ummah sunce basuga Nu'aymah ba, an kuma shiga ɗakin su Yusrah da ƴammatan sashen yayun su Nu'aymahr nanma babu ita, sai su kaɗaine da sauran ƴammata sa'anninsu na gidan da baƙi. Sake dawowa sukai Sashen Addah aka duba ko ina nanma dai babu ita, suka koma sashen Hajjo nanma haka. Zuwa yanzu kam hankalin kowa ya fara tashi, dan ko sallar Asuba wasu sun kasa samun nutsuwar yinta.       Duk da ba'a tunaninta a sashen samarin gidan haka dai aka shiga canma ko za'a dace. amma kuma bata nan. Yanzu kam dai kowa ya tabbatar Nu'aymah bata gidan, samarin gidan dasu Baba malam duk sun dawo massallaci suma an haɗu anata taraddadi, sai sake tambayar su Yusrah da akasan suna tare akeyi da Adawiya data dage take rusar kuka tamkar ranta zai fita.        Gari ya waye tangaran, waɗanda basuyi sallaba suka samu sukaje suka yiyyyi batare da hankalinsu na tare da suba. Umm kam tama kasa magana sai ajiyar zuciya da taje faman sauke a jajjere. Shi kansa Baba Malam binsu kawai yake da kallo. Hajjo tuni ta fara kuka itakam. Ango Abdallah kam nasa tashin hankalin ai ba'ama magana, danshi ya dage sai sake bin ɗakunan gidan yake lungu da saƙo yana dubawa.        Kamar wasa saiga ƙarfe 11am ta buga babu Nu'aymah babu mai kama da ita, saima cin karo da akayi da takarda a jikin Windown ɗakinsu an ajiye. Sai kayanta ƙwara huɗu da alamu suka nuna jehosu akayi ta Windown maybe.         Nanah ce taga takardan, dan haka ta nufi inda su Baba malam ke tsaye da sauran ƴan uwansa ta miƙa musu da faɗa musu inda ta gani. Abban Adawiya ne ya amsa takardan daga hannun Nanah, ya buɗe yana gyara tsayuwarsa. Duk idanu su Baba malam suka zuba masa da ƙaguwar sonjin minene a ciki.         Assalamu alaikum iyayena.                  Kuyi haƙuri da abinda zaku wayi gari da shi daga taskar kuskurena, wlhy yanzu bana son Yah Abdallah akwai wanda zuciyata keso. Nasan babu wanda zan faɗamawa a cikinku ya fahimceni balle akai ga yarda, amma wlhy ina masifar son Ameer fiye da yanda kuke zato da tsammani. Banason na wahalar daku wajen ɗauramin aure da Yah Abdallah nazo kuma na zama sanadin ɓata zuminci da aka gina tunkan samuwarmu daga baya, shiyyasa na zaɓi bin Ameer mu gudu, shi kuma ku aura masa wata a cikin ƴan uwana. Na muku alƙawarin idan komai ya lafa zan dawo gareku ku ɗaura mani aure da masoyina Ameer. Ina fatan bazakuyi fushi dani ba dan ALLAH 🙏🏻😭.            Na barku lafiya. Daga ɗiyarku Zainab Sooraj Hashim (Nu'aymah). ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 ____________________________         Tsit wajen yayi babu wanda ya iya ko ƙwaƙwaran motsi, Baba malam sai faman kaɗa kai yake kawai zuciyarsa na kaikawo.       Hajjo ce ta ƙaraso wajen ganinsu cirko-cirko. “Lafiya? Na ganku cirko-cirko? Ko anji labarin inda take ne?”.        Duk kasa bata amsa sukayi, hakan yasa ranta ɓaci ta daka musu tsawa. “Wai kuna cikin hankalinku kuwa? Ina magana kunmin shiru kai ɗan Malam” ta ƙare maganar idonta akan Baba Malam (Abban Nu'aymah) dan bata faɗar sunansa saboda shine na fari, sai dai tace ɗan Malam.        “Kiyi haƙuri Innah, da kanta ta gudu”. “Ban gane da kanta ta gudu ba? Kana haukane?”. Kasa amsa mata yayi, dan shi kaɗai yasan kalar tashin hankalin da yake ciki a halin yanzun.       Abba Musbahu ne yace, “Innah inaga muje ciki, wannan ba maganar nan baceba”.  Zata sake magana ya kama hannunta suka nufi sashenta tacan baya inda falon mahaifinsu yake. Bin bayansu su Abban Abdallah sukayi, Baba Malam dai bai iya motsawa ba har tsahon wasu mintuna kafin ya bisu.            Bayan haɗuwar duk wanda ya kamata a falon, Abba Musbahu ya sake maimaita abinda ke a rubuce a takarda, wadda Nu'aymah ta ajiye kamar yanda kowa yaji.         “Kai wannan zancen ban yarda da shiba, ina Zainabu taga wayon wani yin wannan iya shegen? Wanene ma Amiru yake ko uwarwa? Tunda muke a gidan nan waya taɓa ganin Zainabu da saurayi ma?”. Hajjo tai magana ranta a ɓace.       Shiru falon yayi, dan kowa yasan maganar Hajjo gaskiyace, babu wanda zaice ya taɓa ganin Nu'aymah da saurayi bayan Abdallah, dan Nu'aymah yarinyace mai shegen tsiwa da rashin tsoro, ko cewa akai ana sonta kai tsaye take faɗin an mata miji a gidansu. Bama ta yarda saurayi yay zuwa biyu wajenta........       “Ina magana kowa yayi shiru, wlhy ni dai ban yardaba, sai dai idan wani munafukine ya sacemin jikata”. Hajjo ta faɗa tana fashewa da kuka.        Baba Malam ne ya kalli Hajjon zuciyarsa na masa zogi, yace, “Innah karki saurin kareta, kinsanfa yaran yanzun ka haifesune amma baka haifi halinsu ba, mudai fara bincikar ƴan uwanta ƙila wani acikinsu yasan Ameer ɗin”.        Girgiza kai Abdallah yayi shima cike da damuwa, “Baba ALLAH koni ban yarda wannan takardar Nu'aymah ce ta rubutata ba, mu dai bincika gaskiya”.          Baba Malam yace, “Abdallah batun ba ita ta rubutaba kam bazai yuwuba, dan wannan rubutun natane, kuma da bakinta a jiya da daddare ta samemu da batun ita a fasa wannan aure ta fasa, bayan mun lallasheta ni da mahaifiyarta ta tafi sai gashi ta sake dawowa daga baya, sannan muna tare da Rudwan, sai dai nasan ganina tare da shi yasa batace komaiba ta gaidasa ta fita. Kaga kenan a lokacin ta silale tabar gidan?”.           Addah tai saurin faɗin, “A'a dan ALLAH Yaya karmu yanke hukunci, mudai bincika ɗin ta bakin Abdallah”.       “Humm” kawai Baba malam ya faɗa zuciyarsa na ƙuna, dukda shima dai wani gefe na zuciyarsa nata masa wasiwasi akan al'amarin.         Yaran gidan duk aka tattaro, sa'anninta su Amal da yayunsu mata harma da ƙannensu mazan da matan. Ɗaya bayan ɗaya aka tambayesu ko sunsan Nu'aymah nada wani saurayi?.        Mafi yawancinsu sunce basu saniba, sai ƙalilan da sukace sun taɓa ganinta kusan sau huɗu da wani saurayi baƙi. Sai dai takance Yah Abdallah ne yake aikosa wajenta.      Da mamaki Abdallah yace, “Ni kuma? Kai gaskiya a'a. Wlhy tunda nake ban taɓa aiko wani wajen Nu'aymah ba sai Ahmad kawai, gashi nan kuma zaune tare damu. danni ko abokaina da yawansu basusan Nu'aymah a ido ba”.       Sosai abin ya sake ɗaure kan kowa a wajen. Adawiya dake sharɓar kuka tace, “Tabbas akwai wani Ameer dake zuwa wajenta, amma acewarsa shiɗin abokin Yah Ab ne, kuma ko jiyama ai yazo wajen walima”.      Duk kallonta sukai. Abdallah yay saurin faɗin, “Wlhy kamar yanda na faɗa ban taɓa aiko kowa wajen Nu'aymah ba, amma k Adawiya zaki iya ganesa ne?”.        Kanta ta ɗaga musu tana sheshshekar kuka.         Hajjo tace, “Nifa gaskiya har yanzu ban yardaba sai naji ta bakin Zainabu, ko naga wata shaida da zata tabbatarmin da cewar guduwa tai da kanta. Kowafa yasan yanda Zainabu keson Abdallahi a gidan nan tunma bata san kantaba, bata tashi nuna mana bata sonshiba sai daren da za'a ɗaura mata aure da shi. Waye ya kawo wannan takardar? A ina kuma ya ganta?”.         Nanah tace, “Hajjo nice na kawo, abayan Windown ɗakinsu na gani an ajiye, kuma harda kayantama a ƙasa”.         “Muje na gani”. Cewar Hajjo tana miƙewa. Sauranma duk tashi sukai suka bita. Kamar yanda Amal ta faɗa haka suka taras, hardama ƙarfen zif ɗin akwati da alamu ya nuna ɓallewa yay wajen rufewa ko buɗewa.       Maigadin gidan baba malam yasa aka kira masa, aka tambayesa ko yaga fitar Nu'aymah a gidan?. Yace shikam bai ganiba, dan tun sha ɗaya da kwata ya rufe gate ma, kuma babu wanda ya sake shiga da fita.        Omar ne ya bada shawarar a duba ta ƙaramin gate na massallaci to. Babu musu akabi shawararsa, da yake yau da asuba ta babban gate duk su baba malam suka fita massallaci sai ga sayin takalma an gani dana akwati. Ƙaramin sayi na mace, sai babba da alama ta nuna takalman mazane, sai sayin jan akwati dake biye da sayin takalman har wajen massallaci, sai dai kasancewar akwai kwalta a titin layin sai ba'aga inda sayin ya tsaya ko ya nufa ba.        Sun dawo cikin gida ana taraddadai saiga wani yaro riƙe da wayar Nu'aymah acewarsa cikin filawoyin massallaci ya gani.       Amsar wayar Abba Musbahu yayi aka hau dubawa bayan anba Adawiya ta cire lock ɗin dan ita kaɗai ta sani. Ana buɗewa a kan WhatsApp aka samu wayarma, cikin kuma inbox ɗin wani datai saving da suna (Sweet Ameer). Scrolling saƙwanin Abba Musbahu yayi ya koma har can farko ya fara karantawa.      Gaba ɗaya hirarrakine tsakanin Nu'aymah da Ameer kuma ta soyayya harma da alƙawarin auren juna kota halin ƙaƙa. Har zuwa saƙon ƙarshe-ƙarshe da duk ya zam na ƙulla yanda zasu gudu ita da shi.      Zuwa yanzunkan kowa jikinsa yayi sanyi, Umm da baba malam sai faman haɗiyar zuciya suke na ɓacin rai, duk da zuciyar Umm sam taƙi gaskata gaskiyar wannan al'amari, dan tafi kowa sanin wacece ɗiyar tata da halayyarta harma da tarbiyyar data bata. Babu abinda Nu'aymah ke ɓoye mata a rayuwa, dai-dai da hira idan tayi ita da Abdallah saita sameta har ɗaki ta bata labari, daga ƙarshe-ƙarshen nan nema take ƙwaɓarta dan kartaje bayan sunyi aure tace zata cigaba dayin hakan. Abinda ya tsoratata a zancen shine sunan Ameer, dan lallai kusan sau huɗu Nu'aymah na kawo abu tace Yah Abdallah ya aiko mata ta hannun abokinsa Ameer, kuma gaba ɗaya saƙwanin har gida yake zuwa ya sameta ya bata. To gashi kuma shi Abdallah yace baida abokima Ameer ɗin balle ya aikosa wajenta. ‘Innalillahi wa'inna ilairraji'un. Mike shirin faruwa da ɗiyarta ne haka? Ya ALLAH ka bayyana abinda ke ɓoye akan wannan al'amari dai cikin sauƙi’. Wannan sambatun Umm keta famanyi a cikin ranta zuciyarta na mata zafi da ɗaci. Yayinda ɓacin ran da take gani shimfiɗe a fuskar mijinta ke sake tada mata hankali.        A yanzu kowa ya yarda Nu'aymah guduwa tayi, sai dai Hajjo dai bata daina faɗin cewar tana wasiwasiba, dan da cataima sai dai idan Ameer wani abu yayma Nu'aymah harta bishi. Babu wanda yabi takan zancenta dan suna ganin akwai ruɗun tsufa tattare da ita.           Ana cikin wannan taraddadi Abdallah yaci karo da saƙon Nu'aymah a wayarsa wanda baisan da shiba. Danshi tunda yay mata magana yaga bata bashi amsaba ya jiya wayar bai sake bi takantaba, tunda da safe kuma an tashi da tashin hankalin rashintane.                       Assalamu alika.     “Yah Ab kayi haƙuri karkaga ban maka adalciba, kasan shi so tsuntsune, gobe ya tashi kan wannan ne ya koma kan wancan. Tabbas na soka a baya kamar babu wasu maza a duniya sai kai kaɗai. Kaima kasan akwai ƙuruciya a kaina a lokacin, shiyyasa sam na kasance bansan Zaɓin daya dace dani. Yanzu kam idanuna sun buɗe ras, zuciyata ta samo zaɓinta. Nasan kozan shekara faɗama iyayenmu bana sonka yanzu bazasu yardaba, bakuma zasu fahimceniba sai sun aura min kai, shiyyasa na zaɓi guduwa, idan komai ya lafa saina dawo a auramin zaɓina. Kaima dan ALLAH ka nema dai-dai kai ka aura kaji. Na barka lafiya Yayana, ina fatan bazaka zauna jirana ba, kuma bazakayi fushiba.          Ƙanwarka Nu'aymah Sooraj Hashim.       Cikin matsanancin fushi Abdallah yay wurgi da wayar hawaye na sulalo masa saman kumatu masu masifar zafi, jikinsa sai rawa yake na ɓacin rai. Dama shi haka yake bai iya fushi ba.         Duk kansa samarin sukayi suna tambayar lafiya?. Kansa ya dafe yana cigaba da kukansa kamar wani yaro ƙarami. yace, “Wlhy ina sonta, amma miyasa Nu'aymah zatamin haka? Minene aibuna dan ina ƙaunarta. Wlhy bazan iya auren kowaba sai ita”.         A tsawace Baba malam ya miƙe yana faɗin, “Dole ne kuwa ka auri watanta a yau ɗin nan Abdallah, ita bata isa kunyatamu ba, bayan mun tara mutane. Inaso daga yau, daga yanzu ka manta da Nu'aymah a cikin zuciyarka har abada kamar yanda nima na manta da ita matsayin ɗiyar cikina”.           Cike da tashin hankali kowa yake kallonsa a falon, dan kowa yasan dama Baba malam yanada zuciya, sannan kaifi ɗaya ne shi, idan yace A dolene A ɗin za'abi, idan yace A'a shima dolene abi............✍ Wannanfa shi ake kira da gaba kura baya sayaƙi😥. Nu'aymah kizo ki bamu gaskiya batu ko masan ina matsalar take ne?.😭            ZAFAFA BIYAR 2021 Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* *_SARAN ƁOYE!!_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* Free page😋 No. 4 WAIWAYE ADON TAFIYA.           Malam Hashim musa shine asalin mai gidan. Babban malami mai tarin ilimi daya taka rawar gani a duniyar musulunci. Yasha gwagwarmaya ƙwarai da gaske na ganin ilimi ya yaɗu da faɗaɗa cikin al'ummarmu ta nagartattun hanyoyi.        Kasancewar yayi gwagwarmayar rayuwarsa ta neman ilimi lokacin ƙuruciya a garin Jibiya ta jihar katsina sai ake kiransa da suna ɗan jibiya.         Matan Malam Hashim ɗan Jibiya biyu kacal a duniya. Zainabu (Hajjo) sai Zulaiha.      Ƴaƴansa Huɗu duk maza, kuma dukansu Hajjo ce ta haifesu, dan har Zulaiha ta koma ga ALLAH bata taɓa ko ɓatan wataba.         Sooraj mahaifin su Nu'aymah da ake kira da Baba Malam shine babban ɗansa. Sai Rudwan mahifin Abdallah wanda shima yanada iliminsa sosai, amma shi yana kasuwanci ne, duk da suma su Baba malam suna kasuwancin. Sai Mustapha Mahaifin su Adawiya, shima dai malamine dan tare da Baba Malam suketa ƙoƙarin cigaba da ginin da mahaifinsu ya bari na yaɗa ilimi. Sai auta Musbahu, shine mahaifin su Yusrah, shima dai malamine, yanama addini hidima yana kuma business.          Kamar yanda kukaji a farko gidansu Nu'aymah gidan manyan malamaine sananne, sannan kuma ƴan kasuwane na gaske, dan har sunada kamfanin dake sarrafa Mangyaɗa da kuma sabulu, suna kuma sufurin kayan masarufi sosai ta hanyoyi daban-daban cikin farashi mai sauƙi duk daga kamfaninsu mai suna ƊAN JIBIYA FAMILY.           Kamfaninsu sanannen kamfanine dake da haja a lungu da saƙo na ƙasarnan sabida sauƙin kayansu. Sannan kuma sanannun malamaine da duniyar musulinci ke alfahari dasu a lungu da saƙo na ƙasarnan. Sunada manyan makarantun da ake koya ilimin addini zallah a cikin kano dama wasu jihohi maƙwafta, suna kuma da gidan marayu nasu na kansu da suka assasa domin ladan ya ringa isa zuwa ga mahaifinsu da ALLAH yayma rasuwa kusan shekaru ashirin da suka shuɗe.      Family ne da alkairansu a bayyane yake wa duniya duk da suna ƙoƙarin ɓoye kansu dan kar asan sune keyi. To amma masu iya magana kance alkairi dankone baya faɗuwa ƙasa banza.            Sooraj (Baba Malam) shine ya zame musu tamkar mahaifi bayan rasuwar Malam Hashim, ya kama ƴan uwansa ya dunƙule kansu waje ɗaya babu mai jin kansu sai ALLAH. Suna ƙaunar junansu matuƙa da mutunta juna. Komai nasu sai sun nema shawararsa kamar yanda shima idan zaiyi wani abu sai ya tarasu ya nema tasu duk da suna a ƙasa dashi.        Tun mahaifinsu nada rai suka gina wannan gida daya kasance gari guda, dan malam Hashim ya mallaki filin ne tun anguwar babu wasu gine-gine kirki, da farkoma noma yakeyi a filin, sai da yaransa suka fara tasawa ya zagayesa yay massallaci da islamiyya, ya kumayi ƙaramin gida a ciki yana zaune da iyalansa. Bayan rasuwarsa arziƙin kasuwancinsu ya ƙara haɓaka sai suka gyarashi aka faɗaɗa massallacin da Islamiyyar, suka kuma ginama kowa sashensa inda zai zauna da iyalansa. A hankali harkoki na ƙara haɓaka musu suna sake gyara gidan har ALLAH ya kaisu ga wannan matsayin suka kasance cikin tsakkiyar birnin kano.      Sooraj (Baba Malam) ya jima baiyi aure ba, dan sai da takai har Hajjo na nuna masa ɓacin ranta akan hakan, sannan yay auren zuminci da wata ƴar ƙanwarta mai suna Salamatu. Rana ɗaya aka ɗaura musu aure su Uku, shi da ƙannensa biyu. Mustapha (Abban Adawiya) da Rudwan (Abban Abdallah) Bayan aurensa da Salamatu ta haifa masa yara uku duk maza. Yayinda shima Rudwan matarsa keda yara uku a lokacin, Maza biyu mace ɗaya. Abdallah shine babba, sai Omar, sai Aysha. Amma Mustapha matarsa bata haihuba.      Shekarar da Musbahu zaiyi aure a shekarar ne Matar Baba malam Salamatu da ƴaƴanta uku, sai matar Mustapha sukai haɗari a hanyarsu ta zuwa Jigawa suka rasu. Lokacin shi Rudwan matarsa na fama da laulayin ciki bata bisuba, sai yaran kawai. Dukansu ALLAH yay musu rasuwa a motar, Abdallah ne kawai keda sauran kwana a duniya. Shima dai ya bugu, dan yasha doguwar jinya kamar bazai rayuwaba ALLAH dai ya raya kayansa bayan yasha wahala. Gida ya koma babu yara ko ɗaya sai Abdallah kawai, sai kuma cikin jikin Momynsa.       Ba ƙaramin tashin hankali suka shigaba a wannan lokacin, dan Hajjo yitai kamar ta zare dan kiɗima, gawarwakin jikokinta biyar da surukanta biyu da driver aka sallata a rana ɗaya kolaci ɗaya, haka aka jera kabirburansu abin tashin hankali😭. (Ya rabbi ka gafartama iyayenmu damu baki ɗaya😭🙏🏻).              Bayan rasuwar matan su Baba malam basu sake maganar aureba har Momyn Abdallah ta haifi cikinta namiji, wanda aka maidama suna Omar, bayan kamar wata biyu da haihuwarta amaryar Musbahu ma ta haihu mace, ita kuma taci suna Jameela.           Hajjo nasan su Baba malam su ƙara aure, amma kuma tausayinsu yasa ta kasa takura musu, sai dai ta cigaba da binsu da addur fatan samun mata nagari da zasu maye musu gurbin matansu. Ansha kawo musu matan aure har gida, musamman kasancewarsu malamai kuma masu kuɗi Alhmdllh. Sai dai basu taɓa amsaba, dan basu farfaɗo daga magagin rashin family ɗinsu ba.        Bayan shekaru biyu da rasa iyalansu ƙwatsam ALLAH ya haɗa Baba malam da Firdausi (Umm) a wajen wani walimar yaye ɗaliban makarantar BUK. Tunda ya ƙyalla ido akanta bai ɗaukeba, duk inda ta shiga ta fita idanunsa a kanta, gashi babu damar mata magana saboda sune manyan baƙi a wajen, hasalima shine yay lecture wa ɗaliban mai ratsa jiki. Inda itama anan Umm ta mutu ason wanda tasan ko kallo batama ishesaba, amma kasancewarta mace miskila ta gaske, kuma mara son yawan magana sai ko a fuska bata nunaba.      Kamar yanda Firdausi (Umm) ta mutu akan son Malam Sooraj Hashim haka babbar ƙawarta, aminiyarta Fauza (Addah) itama ta mutu akansa lokaci guda, sai dai itama ɗin dai bakinta bai furtaba, sai dai kasancewarta mace mai faranfaran da barkwanci dason jama'a sai taita yabashi har Firdausi ta gaji tai mata ƙorafin ta isheta. Dariya tayi a wancan lokacin, dan itace kaɗai ta iya zama da Umm kasancewarta mace mai bahagon hali, ga rashin son wasa, dan sam Umm bata da fara'a, bakuma tason yawan wasa kamar ƙawarta Fauza (Addah).           Ahaka taro ya tashi lafiya Fauza da Firdausi na begen abinda basa tunanin zasu samu a zukatansu, sai dai kuma abinda basu saniba shine Malam Sooraj tunkam yabar makarantar yasa ake bibiyar masa Umm, har aka tashi kowa ya kama gabansa ana binsu a baya har gida anguwarsu. Mai bin nasu yana ganin inda suka shiga ya koma da baya yaje ya sanarma Malam Sooraj Hashim. Baba malam yaji daɗi matuƙa, bai kumayi ƙasa a gwiwa ba ya sake sakawa aka bincika masa mahaifin Firdausi (Umm).             Firdausi (Umm) da Fauza (Addah) ƙawayene konace aminai. Anguwarsu ɗaya, hasalima katangarsu ɗaya, sannan iyayensu Aminaine tun zamanin ƙuruciya. Hakanne ya saka iyayensu matama zama ƙawaye na ƙut da ƙut da babu maijin kansu. A taiƙace ma dai sun zama ƴan uwa. Umm itace ta sakama Fauza suna Addah, saboda sunan babbar yayarsu kenan itama, suna kiranta Addah, shine itama sai take cema ƙawarta Fauza Addah, ahankali suma sauran ƴan gidan suka koma kiranta Addah.        Mahaifin Fauza (Addah) yafi na Firdausi (Umm) arziƙi, dan yana ɗaya daga cikin ƴan kasuwar leda da akeji dasu a cikin kano a wancan lokacin, sannan kuma ɗan boko ne sosai. Mahaifin Fauza (Addah) shike ɗauke da nauyin karatun Umm tun daga firamare har zuwa jami'a. Dan yayun Umm duk iya aji shida na firamare babansu ya ciresu yay musu aure. Itako tana bala'in son karatu, musamman da taga Fauza (Addah) zata cigaba dayi, tata roƙon baban ya barta amma yaƙi, yace itama aure zai mata kamar yayunta. Hankalinta ya tashi, dan haka ta nufi mahaifin Addah ta sanar masa. Shine ya lallasheta, ya kumace ta kwantar ta hankalinta indai karatune zatayi insha ALLAH, shinema zai ɗauki nauyin komai na karatun nata har sai iya inda ta gaji ita da Addah.     Taji daɗi sosai, dan tasan indai yayama babanta magana bazai musaba saboda ƙaunar da sukema juna. Ilai kuwa, baban Addah nama baban Umm magana ya amince, atare aka kaisu makarantar sakandire, bayan sun kammala kuma suka nufi jami'a duk da Mahaifin Umm baiso hakaba, amma kunyar amininsa ta hanashi yin magana ya zuba ido.     To da yake komai aka sakama rana zaizo ƙarahe sai gashi cikin hukuncin ALLAH sun kammala, a randa suka kammala ɗin kuma Umm tai gamo da mijin aure. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 ____________________________         Bayan kwana biyu da haɗuwar Umm da Malam Sooraj Hashim Jibiya yazo har gida da kansa wajen babanta ya nema izinin yin magana da ita, tare da tambayar ko an mata mijine?.      Baban Umm yaji daɗi sosai, dan babu wani mahaluki dazaiƙi jinin gidan Malam Hashim Jibiya, nagartaccen gidan dake cike da nagartattun mutane, manyan malamai da ake alfahari dasu a ciki da wajen ƙasarma gaba ɗaya.         A take babu wani jan zance ya amsa masa da ya nema so wajenta, inhar tana sonsa shikuma yayi alƙawarin aura masa ita. Malam Sooraj (Baba Malam) yayi farin ciki da wannan karamci, haka ya koma gida cike da ɗokin wannan al'amari, da tarin godiyar UBANGIJI kuma. A ranar baiyi magana da Umm ba, sai bayan kamar kwanaki biyu ya sake dawowa gareta. Inda akai masa masauki a gidan su Addah, a falon babansu.      Duk da Addah tayi murnar ganinsa a gidansu sai bata zaƙeba har saida taji dalilin zuwan nasa. Jikinta yayi sanyi hartasha kuka jin ba wajenta yazo ba. Dan tun ran walimar yayesu zuciyarta sam bata huta daga begensaba, tanason faɗama ƴar uwarta Firdausi (Umm) amma takasa furtawa, duk sanda ta tunkareta da zancen sai taji gabanta na faɗuwa.        A yau da taji ƴar uwarta yake so saita godema ALLAH da bata furta mata zancenba, ta kumayi alƙawarin mantawa da Malam Sooraj Hashim jibiya a ranta har abada, dan tafi ƙauna da farin cikin ƴar uwarta ta samesa fiye da ita. Haka ta cire komai a ranta taita ƙoƙarin mantawa da shi, ta kuma cigaba dama ƴar uwarta addu'a da murnar samunsa matsayin mijin aure.            Tun daga wannan ranar Addah bata sake zama tayi koda tunanin Malam Sooraj ba har aka ɗaura musu aure da Umm. A ranar da aka kai Umn gidan Malam Sooraj Hashim Jibiya, aranar Addah tai gamo da Malam Mustapha ƙaninsa da yazo ɗaukar amarya. A take shima soyayyar Addah ta shigesa, baiyi ƙasa a gwiwa ba kuma ya sanarma ɗan uwansa. Kamar yanda yabi nasa neman auren bisa matakin shari'a haka ya bima ƙaninsa har iyayen Addah suka amince suma.          Kwatanta muku kalar farin cikin da Addah da Umm suka shiga a wannan lokacin ɓatama lokacine, sunyi kuka sunyi murna har basu san adadiba, ba ƙaramin godiya sukaima UBANGIJI ba daya sake dunƙulesu a gida ɗaya matsayin matan yaya da ƙani. Itama Addah ba'aja wani dogon lokaci ba aka ɗaura aurenta da Mustapha aka kawota.        Da farko ganin kan Addah da Umm a haɗe yake ya saka Momyn Abdallah jin haushinsu, ta ware kanta bata shiga cikinsu duk da ɗanta Abdallah kullum yana wajen Umm. Dan tunda tazo gidan yazama ɗan ɗakin amarya, ahankalima ya dinga zare kayansa yana komawa dasu sashen Umm. Tun Momynsa na faɗa harta haƙura ta zuba masa ido kawai. Daga baya kuma ma saita kwantar da hankalinta suka ƙulle kansu su huɗu ganin Addah da Umm basu da damuwa. Ita dama matar Abba Musbahu babu ruwanta, dukansu tana girmamasu da mutintasu kasancewarsu matan yayun mijinta. Duk da kuwa bazasu girmetaba sai dai suyi sa'anni ma. Ita kanta Momyn Abdallah ba girmarsu zataiba, kawai dai an mata auren wurine saɓanin su da duk sunyi karatu.          Addah ta samu ciki da zuwanta gidan, amma Umm shiru kakeji. Sunyi murna sosai da cikin Addah, har ALLAH ya sauketa lafiya ta haifo ɗanta Namiji santalele. Wanda yaci suna Hashim, amma suna kiransa da malam ƙarami. Babu jimawa matar Musbahu ta haifo nata cikin itama Namiji, yaci suna Ahmad. Itama tsakaninsu babu nisa da Momyn Abdallah datai haihuwa ta biyar, itama ta haifo mace aka sake maida mata Aysha.       Sosai su Baba malam sukai farin ciki family ɗinsu ya dawo kamar da. Inda sukema Umm Addu'ar itama ALLAH ta kawo mai albarka. Haka haihuwar matan gidan ta cigaba da tafiya a jajjere. Sai da sukai haihuwa hurhuɗu kafin ALLAH ya bama Umm ciki itama. Kowa ya tayata farin ciki sosai, musamman ma Addah da ayanzu takeda yara huɗu, Ɗaya namiji Uku mata. Sai Momyn Abdallah nada huɗu, maza biyu mata biyu. Matar Abba Musbahu nada huɗu itama duk maza.       Umm ta haihu Namiji sannan su Addah duk suna fama da laulayi ƙananun ciki, sai dai kuma kwanan jaririn Uku ya koma. Sosai Umm tasha kuka, amma daga ƙarshe saita share hawayenta dan tasan ALLAHn daya bata ya karɓa ya fita sonsa. sannan ma yaran gidan babu wanda kemata shamaki da nasa, faɗi tashinsu sukeyi a sashenta kamar nata, musamman ma Abdallah da ƴaƴan Addah da inba faɗa maka akaiba bazaka taɓa sanin ba nata baneba.      Cikin amincin ALLAH bata rufa wata uku da haihuwa ba saiga wani cikin, inda shima Baba malam yay murna matuƙa fiye ma dana farko. Su Addah sun rigata haihuwa. Matar Abbah Musbahu ce ta fara haihuwar ƴarta mace da taci suna Yusrah, sai Addah ta haihu itama mace, aka saka mata Adawiya, sai Momyn Abdallah ta haihu itama dai mace, aka saka Safiyya sunan mahaifiyarta, sai dai ana mata alkunya da Amal. Bayan haihuwarsu da watanni itama Umm ta sake haifo ƴarta mace mai kama da ita. Wadda taci suna Zainab, da yake sunan hajjo ne sai ake mata alkunya da Nu'aymah.       Bayan haihuwar Nu'aymah da kusan shekara biyar Umm ta sake haihuwar yaro ɗaya namiji Muhammad, daga nan kuma shiru kakeji bata sake ko ɓatan wata ba. A lokacin Addah ta sake haihuwa uku, mata biyu da namiji ɗaya. Sai yazam tana da yara bakwai. Mata shidda maza biyu. Itama Momyn Abdallah ta ƙara biyu ƴammata tagwaye, tanada mata huɗu maza uku itama. matar Abbah Musbahu ko ɗaya ta ƙara shima namiji, tanada maza biyar mace ɗaya kenan. Daga haka haihuwar ta tsaya musu su duka babu wanda ya ƙarayi.       Rayuwar gidan tacigaba da gudana cike da birgewa da ban sha'awa, inda ALLAH keta ƙara ɗaga darajar mazajensu ta ɓangaren yaɗa da'awa da ilmantar da bayin ALLAH da taimakonsu ta hanyoyi da dama. Suma kuma ba'a barsu a bayaba wajen yima addini hidima. Ƴaƴansu sun tashi kansu a haɗe cike da tarbiyya kula. Komai tare ake musu.        Akwai shaƙuwa sosai tsakanin Abdallah da Nu'aymah, dan tunda aka haifeta ya kasa ya tsare. Komai yaci sai ya ragema Nu'aymah duk da alokacin yayi girma sosai, dan harma ya kammala firamare yana shirin shiga sakandire. Babu mai dukan Nu'aymah ya kwana lafiya a gidan. Umm ce kawai yake ma ɗan kawaici, itama zaita fushi da itane koda bazaiyi maganaba. Komai ma Abdallah na Nu'aymah ne, firarsa Nu'aymah, fushinsa sai an taɓa Nu'aymah, kukansa sai Nu'aymah na kuka.       Itama kamar tasan abinda yake yi, tanama kowa ƙiwa a gidan amma banda Yah Ab, duk abinda ta samu saita rage ta ajiye masa. Tun kowa na ɗaukar lamarin nasu wasa har aka fahimci yafi ƙarfin wasan aka koma binsu da addu'a.          Nu'aymah nada shekaru tara a duniya su Baba malam suka buɗe kamfanin mangyaɗa a garin Lagos, hakan yasa dole Malam Rudwan Hashim Jibiya (Abban Abdallah) ya koma can da iyalansa dan ya dinga kula da shi. Lokacin komawar tasu kam anga tashin hankali wajen Abdallah saboda rabuwa da Nu'aymah. Da ƙyar aka yakicesa daga jikinta, danfa shi yace inhar zaije sai dai da ita, kokuma a barsa anan wajensu. Ganin yanda yay matuƙar ɗaga hankalinsa yasa Hajjo sakawa a barsa nan gida badan Momynsa tasoba. Idan anyi hutu ya ringa zuwa musu, idan kuma sunzo shikenan.         Haka yana gani iyayensa suka lula Lagos aka barsa a kano saboda Nu'aymah. Bayan tafiyarsu Abban Abdallah da shekar biyu shima Abba Musbahu daya ƙara auren mata ta biyu ya bisa tare da Ammin Ahmad, yabar amaryarsa anan gidan yana zuwa weekend, dan aiki yayma Abban Abdallah yawa acan shi kaɗai, ga harkar Addini gata kasuwanci, ga nashi kuma yanayi shima.       Gida sai ya koma daga hajjo sai Umm da Addah da Ummah amaryar Abba Musbahu. Iyalan Baba Malam dana Abba Mustapha kenan. Sai idan sun sami hutune matan kanzo da yaran nan suyi, sukuma su Abbah sai suke zuwa weekend idan matan nasu sunzo nan.         Haka rayuwar ta cigaba da tafiya, shaƙuwa na sake ƙulluwa tsakanin Nu'aymah da Abdallah, hakama tsakanin Adawiya da Nu'aymah, dan sun taso sa'anni su biyu tunda su Yusrah suna Lagos.      Komansu tare ake musu, babu maijin kansu, Hassana da Hussaina ma ake kiransu saboda shaƙuwa. A hankali Adawiya ta kwaso kayanta ta dawo ɗakin Nu'aymah dake sashensu, suka zama a ɗaki guda, makaranarsu ɗaya, ajinsu ɗaya. Kai komaima nasu ɗayane. Gefe ga soyayyar Nu'aymah da Abdallah, inda itama Adawiya son Abdallah keta mata saƙa a zuciya batare da kowa ya saniba har ita kanta. Bata tashi farga dason da take masaba sai da yay mata babbar illa a jini da zuciya, har takai bazata iya haƙura ta barma Nu'aymah ba.          Tunda Abdallah ya kai minzalin aure bayan kammala karatunsa na degree aketa fama da shi yayi aure amma yaƙi, acewarsa Nu'aymah yake so. An lallaɓashi akan ya auri wata idan Nu'aymah ta isa saiya ƙara da ita, amma sam yace bazata saɓuba, zai jirata ko shekara nawane. Abin ya bama kowa mamaki, dan lokacinma fa Nu'aymah da Adawiya suna firamare aji shidda ne. Haka kowa ya haƙura aka zuba masa ido, sai ma ya koma karatu da kasuwancinsa na kansa daya ƙirƙira, ya duƙufa wajen faɗaɗa karatunsa na addini kuma tamkar iyayensa.            A wannan shekarar Abban Abdallah ya sake komawa Abuja da zama inda canma suka buɗe reshen Company ɗinsu na mangyaɗa, sai aka bar Abba Musbahu a Lagos. Tunda suka dawo Abuja Momyn Abdallah ta fara jan yaronta jikinta sosai, a hankali ta janye ra'ayinsa ya koma Abuja da zama wajensu, inda harkokin kasuwancinsa suka fara faɗaɗa daga Nigeria zuwa ƙasar Saudia. Lokacin kuma Adawiya da Nu'aymah sun shiga sakandire.      Suna aji uku a secondary Abdallah ya koma kara faɗaɗa iliminsa na addini a ƙasar Saudia inda yake kasuwancinsa yanzu, sai yazam baya zuwa sai dai aiko da kaya Nigeria Omar da Ahmad na kulawa dasu suma suna aika masa na Nigeria can.               Nu'aymah yarinyace ƙyaƙyƙyawa fara masha ALLAH, dan tana kama da mahaifiyarta sosai, yarinyace mai shegen wayo ga rashin tsoro ga tsiwa. Tsula tsiyarsu suke ita da Adawiya fiye da zato, kullum cikin jan faɗa suke a makaranta daga boko har islamiyya. Duk da rashin jinsu yarane masu kaifin basira da hazaƙa musamman ma Nu'aymah, tana da matuƙar ƙoƙari, dan tun tana aji biyu na secondary tayi saukar Qur'ani, bayan tayi da shekara ɗaya itama Adawiya tayi. Bayan duk sunyi sauka suka juya hadda, tare da karatun sauran littatafai kuma.      Hazaƙar Nu'aymah a makaranta yasa suna aji biyar wani malami ya bada shawarar a barta kawai ta zana ssce a wannan shekarar, koba komai zata kammala jami'a da ƙarancin shekaru. Baba malam ya amshi wannan shawarar, musamman daya duba maganar auren Nu'aymah da Abdallah da kowa ke jira, ya yanke shawarar tana zana ssce za'ayi auren sai taje ta cigaba da karatunta a ɗakin mijinta kawai. amma saiya sa suyi ssce ɗin tare da Adawiya. Wannan shine ya sakasu gama makaranta a wannan shekarar. Adawiya dasu Amal nada shekaru sha bakwai cif, Nu'aymah kuwa bata cikaba har yanzu, tana sha shida da wasu watanni dan su Adawiya sun girmeta...............✍   ZAFAFA BIYAR 2021 Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* *_SARAN ƁOYE!!_* *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* Free page😋 _Daga yau free pages sun ƙare masoya. Ku garzayo domin samun waɗanan littatafai guda biyar akan farashi mai sauƙi. Dan girman ALLAH kibi ta hanyar data dace ki mallaki naki😅, karki zama cikin masoya masu mana SARAN ƁOYE akan kasuwancinmu😢🙏, muna alfahari daku aduk inda kuke. Muna godiya kuma da ƙaunar da kuke nuna mana irin trillions ɗin nan. Idan nace ku na dabanne ina nufin na daban har cikin raina😘😘🤝🏻_. *_Masu buƙatar mu saka musu tallar kayan sana'arsu zasu iya zuwa suyi magana damu domin tayasu tallata hajojinsu a yanar gizo😘🤝🏻_*. No. 5 .................“Indai har a yau dole sai an ɗaura auren Abdallah da wata kamar yanda Yaya Malam ya faɗa, to kuwa sai dai a ɗaura masa da ɗiyar ƴar uwata Nusaiba!!”.         Abban Abdallah dake shirin fita wajen ɗaurin aure ya tsaya cak daga ƙoƙarin saka maɓallin rigar farar shaddarsa ƴar ciki yana kallon Momy ta mirror. Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya cigaba da abinda ya keyi.         Ƙarasa shigowa cikin ɗakin tayi ta tsaya a bayansa cike da damuwa. Sai da ya gama saka maɓallin guda uku sannan ya ɗauki babbar rigar itama ya warware zai saka. Saurin riƙe rigar Momy tayi hawaye na zubo mata saman fuska. Yanzu kam kallonta yayi da ƙyau yana ƙoƙarin haɗiye damuwarsa. “Na zata mun gama wannan maganar tun shekaru uku da suka shuɗe Khadija”.       Sosai ta fashe masa da kuka yanzun kam tana kallonsa cikin ido, “Abban Abdallah dan ALLAH ka fahimcen......”. “Anƙi a fahimcekin Khadijah!!”. Ya faɗa a tsananin tsawace jikinsa har yana rawa. Ya fisge rigarsa dake a hannunta tare da nuna mata hanya alamar ta fice masa a ɗaki.        “Abban Abdal.......” “Khadija!!!”. Ya kira sunanta da tsawa fiye dana farko. Baya taja a firgice ta manne da bango, sai kuma ta fashe da kuka bakinta na rawa alamar tanason yin magana amma tana shakka.     Tsaki Abba yay ya jefa babbar rigar saman gado yay ficewarsa ya barta a ɗakin. Can bayan ɗakunansu ya zagaya yanata huci. (nace, “Ashe ba Baba malam bane kawai mai zuciya a gidan😂).         Zubewa ƙasa Momy tayi tana kuka abin tausayi, kusan mintuna huɗu da fitar Abba akai Knocking ƙofar dayin sallama. Saurin share hawayenta tayi ta miƙe tsaye jin muryar Abdallah. Sai da ta kalla kanta a mirror ta sake cirar tissue ta gyara fuskar da ƙyau sannan ta amsa masa sallamar da bashi izinin shigowa.       Jikinsa a sanyaye ya shigo, ya ƙaraso cikin ɗakin sosai idanunsa akan mahaifiyarsa da itama kallonsa take cike da tausayawa. Matsowa tai da sauri kafin ya ƙaraso, ta kama hannunsa ta zaunar a bakin gadon tana faɗin, “Abdallah kana lafiya dai ko?”.            “Momy bana a lafiya wlhy”. Ya faɗa tamkar zai fashe da kuka. Murmushin ƙarfin hali Momy tayi, kusa da shi ta zauna tana ƙoƙarin haɗiye tata damuwar. Ta kamo hanunsa cikin nata ta rumtse. “Abdallah nasan dole ka tsinta kanka a cikin ruɗani game da wannan al'amarin, sai dai dan ALLAH ka kwantar da hankalinka kaji, kasa a ranka haka shine mafi alkairi shiyyasa ALLAH ya ƙaddara hakan. Nu'aymah ba ita bace autar mata, bakuma dama an halicceka domin ita kawai bane ba........”       “Momy karkice haka, wlhy ina son Nu'aymah sosai, da sonta na rayu tun ban gama sanin ciwon kaina ba. Amma dan ALLAH Momy ki faɗamin inada wani haline mara ƙyau da zaisa Nu'aymah ta ƙini?”.     Murmushi Momy tayi, takai hannu saman kumatunsa ta shafa. “Baka da wani aibu Abdallah na, babu wata mace da zaka tunkara da kalmar so ace ta gujeka. Itama ƙuruciya ce da rashin sanin ciwon kai ke ɗawainiya da ita. Shawara ɗaya zan baka shine ka kwantar da hankalinka, ka cigaba da addu'a kuma, inhar Nu'aymah alkairi ce a gareka, ALLAH kuma ya ƙaddara zata kasance cikin matanka ALLAH ya dawo da hankalinta gareka. Idan kuma ba alkairi bane aurenta ALLAH ya cire maka ita a zuciyarka kaji. Zan tayaka da addu'ar nan nima insha ALLAH”.      Kansa ya ɗaga mata hawaye na sulalo masa a ido ɗaya. Momy ta saka babban yatsanta ta ɗauke masa shi tana murmushi. “Banason ganin wannan hawayen Sweetheart kaji”. Nanma kai kawai ya jinjina mata yana haɗiye tsantsar damuwarsa.       “To amma Momy ni banason a auramin kowa, a bari kawai zan jira Nu'aymah. Na roƙi Baba Malam hakan amma yaƙi saurarena, nasa Abba ma bazai saurareniba tunda basa tsallake maganar Baba malam”.        Shiru Momy tai kamar wadda ta tafi tunani, sai da Abdallah ya ɗan taɓata da kiran sunanta sannan ta sauke gajeren numfashi da kallonsa. “Abdallah kaima ka sani babu wanda ya isa canja abinda Yaya Malam ya faɗa a gidan nan, ko Hajjo goyama duk abinda ya sharɗanta baya takeyi. Babbar damuwata kar ace za'a aura maka cikin ƙananun yarannan Yusrah ko Adawiya, dan kaga dai Hajarah da Kubrah duk sunada samarinsu kuma kowa yasani a gidan nan, tunda har an tsaida magana, jira kawai ake su kammala karatunsu a ɗaura musu aure. Abdallah kullum shekaru kake ƙarawa ba ƙuruciya ba, ka kai minzalin da ya kamata ace ka ajiye iyali tuni, da ace baka zauna jiran gawon shanu ba da yanzu ɗanka ko ƴarka zai kai shekara biyar koma fiye da haka Abdallah. Abdallah dubeni tsufa fa nakeyi, ina buƙatar jikokina kamar yanda nasan kaima kana buƙatar mace tare da kai. Ya kamata ace ka auri yarinyar da zata iya kula da duka ɗawainiyarka ba wadda zakai tunanin zaman raino ba Abdallah. Kayi nazari akan maganata ka ɗaurata a mizanin fahimta. Aysha, Sumayya, Badariyya, Maryam duk ƙannanka ne a gidan nan, amma ka duba shekarunsu nawa da yin aure?, dukansu sunada ƴaƴansu abin sha'awa, duk da matane ba kamar kai namiji ba”.         “Momy duka na fahimci maganarki, to amma kinga nima ai bansan wadda zasu aura mani ɗinba, amma nasan Abbah ya sani, ki tambayesa kozai sanar miki?”.        “Bazai sanar mini ba Abdallah, sai dai kaine nakeson ka kawoma kanka mafita”. “Mafita kuma Momy? Tami?”.       Numfashi ta sauke tana sake kallonsa da ƙyau. “Abdallah kaje ka samu Baba malam ka sanar masa ka yarda su aura maka duk wadda sukaga ta dace, amma su haɗa maka da Nusaiban Fatima {Gwaggonka}”.         “Momy Nusaiba kuma? Momy baki haƙura da zancen nanba dama? ALLAH ni bantaɓa jin Nusaiba a rainaba Momy, ina mata sone na ƙanwa kamar yanda nakema su Aysha”.          “Abdallah basai kaso Nusaiba ba yanzun, idan kukai aure tana gidanka a hankali zaka fara sonta. Yarinyarnan ƙyaƙyƙyawa ce itama, sannan tanada tarbiyya da hankali kaima ka sani ai”.      Shiru Abdallah yay kawai yana kallon Momy, a cikin ransa sai faman faɗin, ‘Nu'aymah kina inane? Dan ALLAH ki dawo gareni, ki taimakeni ki ceci zuciyar da bata taɓa fashi a ƙaunarki ba, ki taimaki numfashin da ke burin rayuwa da naki har abada. Nu'aymah miyasa kika kasancemin mai SARAN ƁOYE ne.........?’           “Abdallah!”. Momy ta faɗa tana girgiza shi. Kallonta yay da sauri dan baiji mitace ba. Zaiyi magana Abba ya shigo ɗakin. Duk da ya gansu sai ya ɗauke kansa kamar baisan da suba, rigarsa ya nufa ya ɗauka yana ƙoƙarin sakawa. Tashi Abdallah yay ya tako zuwa gabansa, taimaka masa yay ya saka rigar sannan ya kallesa. Zaiyi magana Abbah ya ɗaga masa hannu. “Banason jin komai Abdallah, kaje ka shirya ka fita massallaci, dan da an idar da sallar Juma'a za'a ɗaura maka aure kamar yanda Yayah ya faɗa”.       Ƙasa Abdallah yay da kansa yana haɗiye zuciya da sauri-sauri, baice komaiba ya juya ya fita idanunsa cike da ƙwalla.       Ɗauke kai Abba yay ya maida ga mirror inda yake hidimar cigaba da shiryawa. Momy kuwa tabi ɗan nata da kallo tamkar zata fasa kuka. __________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 ______________________           Masu posting a facebook dan ALLAH wannan roƙonane a gareku dama na WhatsApp da ko ina.. Nasan duk masoyin ƙwarai nason cigaban masoyinsa. Tabbas soyayyace ta sakaku kai littafina can, kuma inajin daɗin hakan da alfahari da wannan soyayya. To amma dan ALLAH ina roƙonku ku tausaya mana banda littatafan mu na ƙuɗi. Kamar wannan SARAN ƁOYE na kuɗi ne, yana cikin ZAFAFA BIYAR 2021. daga yau kuma free pages sun ƙare, gamai buƙata yazo ya biya naira 300 kacal sai ya cigaba da samu dan girman ALLAH Masoya amana adalci🤓😥🙏🏻. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 ____________________________             Hankalin Umm a tashe yake matuƙa gaya, taƙi yarda ta fita wajen ƴan uwanta balle ta sanar musu halin da ake ciki. Tunda Baba Malam da yaƙi saurarenta itama ya fita bayan yayi shiri taketa kai kawo a ɗakinsa. Lokaci zuwa lokaci tana share ƙwallar dake ziraro mata.         Sam zuciyarta ta kasa yarda Nu'aymah guduwa tayi da kanta. Tasan wacece ƴarta, tasan tarbiyyar data bata. To amma a yanda al'amarin ya zone babu ta inda ita kanta zata iya bama Nu'aymah kariya koda a wajen mahaifinta ne. Balle kuma sauran jama'ar gidan. ‘Shin miya samu yarinyarta ne? Ta yaya tabar gida?’ tai maganar a fili tana fashewa da kuka maiban tausayi.         “ALLAH sarki Umm kiyi haƙuri ALLAH na nan😭🚶🏻”. ___________________________________                  Gaba ɗaya yanayin shagalin bikin a cikin gida ya canja, mazane kawai a waje da basusan mike faruwaba keta walwalarsu. Hakama abokan Abdallah sai faman fantamawa suke cikin farar shadda datai bala'in musu ƙyau.       Sai da aka fara gabatar da sallar juma'a kafin a ɗora da ɗaura auren da yazoma mutane da saɓanin abinda suka gani a jikin invitation card.          Ba mutanen waje kawai ba, hatta ƙannen Baba Malam su Abba sai da sukasha mamaki matuƙa da yanda ɗaurin auren yazo. Dan kuwa ɗaurin auren yazo musu ne a yanda basuyi tunani ko tsammani ba.        An ɗaura auren Abdallah Rudwan Hashim Jibiya da Yusrah Musbahu Hashim Jibiya akan sadaki naira dubu ɗari. Sai aka sake ɗaurawa da Adawiya Mustapha Hashim jibiya, da Abdallah Rudwan Hashim Jibiya shima akan sadaki naira dubu ɗari. Aka ɗora da doguwar addu'ar fatan zaman lafiya ga ma'auratan daga ƙarshe.       Babu wanda ya iya magana a cikin su Abbah, dan kuwa su duk abinda Baba Malam ya zartar akansu bama ƴaƴansu ba basu da ja. Sun gama bashi darajar Uba tun tuni, sunsan bazai cutar da suba balle kuma ƴaƴansu. Fatansu kawai ALLAH yasa hakan shine mafi alkairi, ALLAH ya basu zaman lafiya kuma. Itama Nu'aymah ALLAH ya dawo musu da ita gida lafiya.           Kan Abdallah neman kwancewa yay dajin wannan al'amari, ko kammala ɗaura auren ba'ayiba ya sulale ya koma cikin gida kansa na wani kalar mahaukacin sara masa, ɗakin Abubakar cikin ƙannensa samarin gidan ya shige ya kulle kansa batare da kowa ya saniba.         Abokansa kansu cikin ruɗani da mamaki suke, sai dai kafin su sami damar tambayarsa suka nemesa suka rasa a wajen. Dole sai tambayar juna lafiya? suka komayi. Amma babu mai bada amsa. ★★★★★★★            Hakama cikin gidan tunda sakamakon ɗaurin aure ya iso kunnuwansu kowa ya kasa motsi, sai kallon kallo kawai akeyi da idanu baki ya gaza furta komai.        Momyn Abdallah jitai kamar an ɗaura mata dutsen dala bisa kai. Tayayama za'a aurama Abdallah aure da yara ƙanana irin waɗan nan har guda biyu?.       Haka taketa ayyanawa a zuciyarta, a fili kam sai laɓɓanta ke motsi maganar ta kasa furtuwa. Sai danginta ne keta ƙananun magana musamman ma Umman Nusaiba.          Yusrah ma tunda zancen ya isa garesu ta yanke jiki ta faɗi a sume, sai da aka yayyafa mata ruwa ta farfaɗo. Kuka take tamkar ranta zai fita. Ta yayama zata auri Yah Abdallah da tasan duk duniya babu wadda yake so sama da Nu'aymah. Sannan Nu'aymah ma na bala'in sonsa da ƙaunarsa. Tunda aka wayi gari da ɓatan Nu'aymah sam bata yarda guduwa tayiba, dan kuwa a daren jiya ana wajen walima ta dawo gida tanason shiga toilet. Motsin mutum taji a ɗakin, amma tana shigowa aka ɓuya bataga ko waneneba. Kashin daya matseta ne yasa batabi takan sanin wanene ba ta shige toilet. Bayan ta shiga ta fito taji motsin fitar koma wanene daga ɗakin. Bataga kowayeba, hakan yasata fita da sauri ta zagaya ta bayan Windows ɗin saboda ƙarar jan akwati da taji kamar anayi tacan. Dan ko ina na gidan Interlock ne. Tana ɓullowa ana barin wajen, sai dai zuciyarta ta zargi mutum ɗaya a lokacin, amma bata da tabbas ɗin da zata fito tace ga abinda ta gani kokuma ga wanda ta gani. Dan babu wata ƙwaƙwaran shaida a hannunta.          Abu na biyu Nu'aymah abokiyar firartace sosai, dan ko suna Lagos takanyi dogon Charting da Nu'aymah fiye da Amal da Adawiya, sannan kusan kullum sai sunyi waya, mafi yawan hirar da Nu'aymah ke mata kuma akan Yah Abdallah ne, dan komai na Nu'aymah da sunan Abdallah a ciki.      Ta sake fashewa da kuka tana ƙanƙame Aminta da itama cikin ruɗanin take. Bawai auren ƴarta da Abdallah ne matsalarta ba, matsalarta yanda al'amarin yazo. Tana ganin kamar Mazansu sunyi gaggawa akan yanke wannan hukuncin. Kamar ya dace ace sun zauna sunyi dogon nazari da bincike akan al'amarin Nu'aymah. To amma ita bata da wani ƙarfin iko akan sakawa ko hanawa a gidan, sai dai kawai ta shiga jerin shiga sahun masu addu'ar ALLAH ya warware al'amarin cikin sauƙi, duk inda Nu'aymah take kuma ALLAH ya kareta ya tsareta, ALLAH ya maido hankalinta gida. ★★★★          Adawiya da ko wanka ta kasayi saboda fargabar wadda za'a mayema Abdallah gurbin Nu'aymah da ita ta miƙe zumbur sanda labarin ya iso kunnenta. Dama a sashensu take tun bayan gama dambarwar guduwar Nu'aymah. Ta daka wani uban tsalle zata ƙwala ihun farin ciki Hajarah yayarta wadda takebi data shigo yanzun tai azamar rufe mata baki.           “Innalillahi, Adawiya minene haka kikeyi? Kefa nagama tamkar murna kikeyi ne ko mi?”.       Janye hanun Aunty Hajarah Adawiya tai daga kan bakinta tana hura hanci, kamar zatai magana cikin masifa kuma saita fasa. Canja yanayinta tayi zuwa damuwa ƙwalla na taruwar mata a idanu. “Aunty Hajarah ki barni nayi ihu ko zanji sanyi a raina, ta yaya za'ace ni Adawiya nice matar Yah Abdallah yau?”. A mamakin Hajarah sai taga Adawiya kuma ta fashe da dariya.         Baki Hajarah ta saki tana kallonta dan al'ajabi. Zatai magana sai ga Addah ta shigo ɗakin.          “K! Wane kalar iskancine wannan?!!”. Ta faɗa da matsananciyar tsawa tana kallon Adawiya data fara taka rawa. Daɓar ta zauna a bakin gado tana ɓata fuska.      Addah ta ƙaraso cikin ɗakin jikinta har rawa yakeyi, jikake “Tasss!!” ta ɗauke fuskar Adawiya da wani bahagon mari haggu da damanta. Kifff Adawiya ta kifo ƙasa dan azaba da gushewar numfashi na wucin gadi.             Cikin tsananin firgici da tashin hankali Hajarah tai tsalle gefe jikinta itama na rawa, tai masifar ware idanu akan mahaifiyar tasu da akan daɗe ba'aga fushintaba a gidan.           Addah tasa hannu ta ɗago Adawiya ta cigaba da bata maruka, sai da tai mata shidda ƙwarara sannan ta hankaɗata kan hado. Sosai wahala ma ta hana Adawiya kuka, sai sauke numfarfashi take tamkar zata shiɗe. Kallon Hajarah Addah tayi, batare da tayi magana na ta nuna mata hanyar fita.          Zabira Hajarah tai ta nufi ƙofar da bala'in sassarfa, sai da taje gab da fita sannan ta tsaya cak saboda tsawar da Addah ta daka mata. “Idan kin fita ki sanar da kowa kinji ko?”. Saurin haɗiye kukan dake neman kufce mata Hajarah tayi, ta kalli mahaifiyar tasu tana mai girgiza kanta. “K....k...kiyi haƙuri dan ALLAH Addah”. Hanya ta sake nuna mata alamar ta wuce. Hajarah bata sake magana ba tabi umarnin Addah ta fice.     ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 ____________________________      Juyawa Addah ta sakeyi ga Adawiya dake kwance tamkar wadda shaƙar iskar numfashi taima ƙaranci. “Tashi dan Ubanki!!”. Da sauri Adawiya ta tashi tanaja baya daga farkon gadon zuwa ƙarshe, jikinta sai rawa yake tana kallon Addah, amma tsabar bushewar zuciya ajiyar zuciya kawai take saukewa taƙi tai kuka.        Addah ta kalleta babu ko ɗigon rahama a fuskarta. “Waye ya taimaka miki a gidan nan wajen ɗauke Nu'aymah?!”.        Sai yanzune Adawiya ta fashe da kuka tana cigaba da kallon Addah. “A...a....Addah ALLAH....”          “Wlhy kikaimin ƙarya Adawiya sai kinyi nadamar sanina. Ina kuka kaita? Ke dawa kuma kukai aikin?”.         Kasa magana Adawiya tayi, sai kukanta dake ƙara ƙarfi tana sake jan jikinta baya. “Bazaki faɗaminba saina tona miki asiri a gaban kowa?!!!”  Addah ta faɗa da tsananin tsawa hawaye na sauka mata a kumatu.      Zabura baya Adawiya tayi itama tana mai fashewa da wani kukan. “Wlhy Addah, w....wlhy bani bace, wlhy bansan komai akai ba”.        “Adawiya ni na haifeki, nasan halinki, ki faɗamin gaskiya wlhy kona yankaki a ɗakin dan ubanda ya haifeki”.        Sake fashewa da kuka Adawiya tayi tana girgiza kanta da ɗaga yatsanta ɗaya sama. “Wlhy Addah kinji na rantse ban aikata komaiba”.          “Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un” Addah ta shiga ambata tana dafe kanta, hawayene masu cike da zafi da ruɗani ke sakko mata a gurguje, ta zube saman gadon itama ta dafe kanta.     Rarrafowa ta bayanta Adawiya tayi ta rungumeta itama tana kukan.... _______________________                Hayaniyar data yawaita a sashen Baba Malam ne ya fara jan hankalin sauran mutane dake a harabar gidan da sauran sassan gidan.       Kafin da yawa suyi yunƙurin shiga sashen sai gashi an fito da Umm wadda ta yanke jiki ta faɗi a sandare alamar babu rai tattare da ita. A take hankalin kowa ya tashi. Omar ne yay azamar nufar motar daya shigo da ita yanzun nan ya buɗe baya aka saka Umm, babu tunanin neman ba'asi ko jiran umarnin iyayensu yaja motar bayan Mahaifiyar Nanah (Gwaggo Safina) ta shiga ita da Gwaggo Hafsat yayar Umm ɗin da take bimawa ya bar gidan a ɗari.      Da yake ƴan ɗaurin aure duk sun tafi zuwa babban Hall ɗin da aka kama domin cin abinci sai ƙofar gidan babu yawan jama'a. Shima Omar daga can baba malam ya aikosa ɗaukar Abdallah da suka fahimci baya tare dasu, ga baƙi nata tambayar ango kuma, musamman ma abokansu Baba Malam ɗin, shine baba malam yace Omar yaje ya ɗakkosa a gida dan yasan Abdallahn bazai wuci gida ya koma ba. To gashi yana shigowa kuma ya iske wannan tashin hankali.        Hajarah ce a firgice taje ta bugama su Addah tana faɗin, “Addah ki fito Umm ta rasu”.            Wani wawan miƙewa Addah tai ta nufi ƙofa bayan ta wancakalar da Adawiya dake kwance a bayanta ƙasa. Ta buɗe ɗakin zuciyarta na wani mahaukacin bugawa. Sai dai kuma bataga Hajarah ba, sannan baƙi dake a ɓangarenta da mafi yawansu ƴan gidansu ne da ƴan Uwan Umm duk sun fice. Batako tsaya sauraren bin ba'asiba ta fice daga gidan, ALLAH ya sota ta samu Napep dake ta jigilar ƴan biki a ƙofar gidan ta shiga, sakawa tai ya ringabin bayan Omar dake zuba uban gudu kamar zai tashi sama............✍ ____________________________         Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?. Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai. Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta WhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauƙi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓. Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* *_Da sunan ALLAH mai Rahma mai jinƙai_* _Ya Rabbi ka bani ikon rubuta abinda zai amfaneni ni da al'umarka, ka tsare harshena da alƙalamina rubuta abinda zai cutar da ni da su😭🙏🏻_. *_Ya rabbi ka gafarma mahaifina masoyina da dukan ƴan uwa musulmai da suka rigamu gidan amsa kiranka😭🙏🏻_* No. 6 ................Baba malam na tsaka da sallamar abokan arziƙinsa kira ya shigo wayarsa. Kamar zai share karya duba sai kuma ya cirota daga cikin babbar rigarsa. Ganin Number da akai kiran da ita yasashi ɗagawa da sauri ya ɗora a kunne yana faɗin, “Assalamu alaikum. Innah!”. Batare da Hajjo ta amsa masa sallamarba cikin kuka take faɗin, “Duk inda kuke ku taho gidan nan babu lafiya ɗan Malam”.        “I...in...innah miya faru halan?”. A zafafe Hajjo tace, “Sai kaji abinda ya faru zaku taho? To Firdausi ce aka fita da ita babu rai”.       Ba ƙaramin bugun ƙirjin Baba malam wannan kalma tayi ba, kafin ya samu damar yin magana Hajjo ta yanke kiran. ‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ Baba malam ya fara ambata akan laɓɓansa, atake damuwarsa da yaketa ƙoƙarin dannewa take ƙoƙarin fitowa fili, ya share zufar data taru masa a gaban goshi yana busar da iska mai zafi. lumshe idanunsa yay na wasu mintuna yana ambatar addu'a. Sai da yaɗan samu nutsuwa sannan ya juya zuwa cikin hall ɗin. Ruwa ya samu ya sha zuciyarsa ta ƙara nutsuwa kafin ya tattara su Abbah da samarin gidan suka bar wajen.         Suna fara tafiya sai ga kiran Omar, shine ya sake sanar masa da abinda ke faruwa, tare da asibitin da suke a yanzu haka. Kai tsaye can suka nufa, inda suka tarar da Addah da yayun Umm sun haɗe kai sunata sharɓan kuka.          Hankalinsu Baba Malam sai ya sake tashi fiye da farko, amma da yake shiɗin kamilin mutum ne sai fuskarsa bata nuna yanda yake a rikice ba. Addu'oi ya keta ambata a ransa yana cigaba da miƙama UBANGIJI kukansa.       Sun kai tsahon mintuna arba'in suna jiran fitowar Doctor kafin ya fito. A kusan tare suka sauke ajiyar zuciya ganin fuskar Doctor ɗin da ɗan sassauci ba kamar ɗazunba. Kallonsu yay cike da girmamawa yace, “Alhmdllh ta farfaɗo. jininta ne ya hau sosai, ALLAH ma ya taƙaita mata wahala, dan irin wannan faɗuwar ga mai hawan jini babbar matsalace, musamman yanda jininta yay ƙololuwar hawa”.         Sake sauke ajiyar zuciya duk sukayi, Baba Malam ya kauda kansa gefe tare da ɗauke ƴan ƙwallar da suka taru masa a cikin ido.            Baba malam ne kawai aka bari ya shiga ya ganta, tana kwance idanunta rufe an saka mata ƙarin ruwa. Tai masa wani irin masifar haske a ido. Ya jima yana kallonta tausayinta na sake faɗaɗa a zuciyarsa, ya kai hannu ya shafa kanta yana magana a hankali. ‘ALLAH ya baki haƙuri Jannat kinji, ALLAH ya bamu ikon cinye jarabawar nan, kiyi haƙuri ki daina damuwa’. Ya ƙare maganar da sumbatar goshinta.        Ya kai tsahon mintuna goma yana cigaba da kallon ƙyaƙyƙyawar matar tasa kafin ya juya ya fita a ɗakin. Gaba ɗaya kan baba malam ya ƙara ɗaukar zafi, gashi dama shima yana da hawan jinin. Gudun kar gazawarsa ta bayyana ya sashi samun Doctor ya nema a sallamesu su koma gida da Umm. Family Doctor ɗinsu zai cigaba da kula da ita.        Doctor baiyi musu ba ya basu sallama, dan yasan su ɗin manyan mutanene, bazasuso cigaba da zama a asibitinba kodan yanayin da ƙasar yake na rashin tsaro.      Bayan kammala duk abinda ya dace aka saka Umm a Ambulance. Addah ta shiga tare da Nurse ɗin da aka basu, su kuma suka shiga motocin da sukazo a ciki. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 __________________ ________________________             Sosai hankalin mutanen gidan da ƴan biki ya ƙara tashi ganin Ambulance har cikin gida. Da yawan gwiwoyin wasu ya sare a zatonsu ko Umm ta rasu ne. Sai da sukaga an fito da ita zuwa sashensu harda ƙarin ruwan da ake mata sannan aka fara sauke ajiyar zuciyoyi da ambaton Alhmdllh.             Bayan an shiga da Umm Bedroom ɗin Baba Malam dangi suka shiga jajantama juna da addu'ar samun lafiya a gareta tare da fatan dawowar Nu'aymah gida cikin ƙoshin lafiya. Daga haka dangi na kusa suka fara zare jiki suna barin gidan, dan kam ko masu gidan basuce dasu komaiba sunsan suna buƙatar a basu wuri suji da abinda ya damesu.        Kafin sallar magriba gidan ya ragu sosai. dan irin dangi na katsina, kaduna, jigawa ma duk sunyi sallama sun tafi tunda ba wani nisa bane mai yawa. Balle kuma ƴan cikin kano da ƴan gayyar aci shinkafa asha zoɓo😏🤐.          Yayun Umm su Maman Nanah dai suna nan basu tafi ba sukam duk da anan cikin kano suke aure su duka. Sai kuma wasu a cikin dangin Momyn Abdallah da suma sukaƙi barin gidan.        Har bayan sallar isha'i Umm nata barci, yau Baba malam ko wajen karatu bai zauna ba, sai Abba Mustapha ne yayma magidantan dake ɗaukar karatu bayan sallar isha'i ƙari. Shima daga ƙarin ya sallami kowa ya shigo gida. ★★★★         Zuwa bayan isha'in ne hankalin kowa ya koma kan sanin ina Abdallah?, dan duk wannan rugun tsumin da akeyi babu wanda yaji ɗuriyarsa. Nemansa aka shigayi a waya amma bai ɗagaba. Hakan yasa samarin gidan suka fara didduba ɗakunansu. Har hankali ya fara tashi na rashin ganin nasa sai gashi Abubakar ya samosa a ɗakinsa yana barci.       Fita yay ya sanar musu. A tare duk suka ɗura kai cikin ɗakin, inda suka sami Abdallah kwance cikin matsanancin zazzaɓi. Da yake Doctor yazo sake duba Umm sai aka kirasa yazo ya duba Abdallah shima. Shikam damuwace ta saukar masa da zazzaɓin, sai kuma yunwa. Magunguna Doctor ya haɗa masa harda wanda zai sakashi barci, yace a bashi abinci ya ci kafin yasha.      Haka kuwa akayi, Hajjo ta basa abinci da kanta duk da yanata cewa shi ya ƙoshi. Da dai lallashi da ban baki aka samu yaci kaɗan yasha magani. Ahmad ne ya taimaka masa yay wanka sannan aka maidasa ɗakinsa da Hajarah ta gyara ya kwanta.      Ganin barci ya ɗaukesa sai duk suka fito, aka barsa da Ahmad kawai da zai kwana tare da shi dan ba'asan mi dare zaizo da shiba. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 ___________________________ ___________________________              WASHE GARI         ___________________                     Daga Umm har Abdallah sun tashi jikinsu Alhmdllh, sai dai damuwa irin ta zuciya da fitarta farat ɗaya bazai yuwuba. Bayan kammala karin kumallo aka haɗu aka tsaftace gidan, sauran baƙi duk suka kama gabansu. Su Sumayya kawai ne duk suna nan basu koma gidajensu ba.          Bayan sallar azhar Baba malam da su Abba suka zauna tare da Hajjo, sun daɗe suna tattaunawa kafin su buƙaci ganin matan gidan suma da Abdallah.       Cikin nutsuwa Baba Malam yay musu bayanin da zasu fahimcesa akan wannan canjin da yayi, da kuma dalilinsa na aurama Abdallah su Yusrah. Ya kuma sake nuna fushinsa sosai akan abinda Nu'aymah ta aikata. Har saida takai ƙannen nasa da matansu na bashi haƙuri.      Umm dai batace da kowa komaiba har aka gama aka sallami kowa. itace farkon tashi ta fice a falon. Dan haka duk suka bita da kallon tausayawa. Banda Baba malam da yay kamarma baisan mi sukeyiba, yanata ƙoƙarin cigaba da danne damuwarsa a rai. ____________________ BAYAN SATI ƊAYA ____________________               Bayan sati ɗaya da faruwar komai gidan ya koma normal a zahiri. A baɗini kuwa kowa shi kaɗai yasan damuwarsa da matsalarsa.      Kasancewar ita Adawiya sun kammala secondary baba malam ya yanke hukuncin Abdallah zai tafi da ita can ta cigaba da karatunta, ita kuma Yusrah saita ƙarasa watannin da suka rage mata sai yazo ya tafi da ita. Kowa yayi na'am da wannan magana, dan harma an kammalama Adawiya duka shirye-shiryen tafiya.      Kwatanta muku irin farin cikin da Adawiya take cikima ɓata lokacine, sai dai tanata ƙoƙarin dannewa saboda tsoron Addah data sanyama duk wani motsinta idanu yanzun, sannan ta daina sakar mata fuska gaba ɗaya..             Ganin yanda Addah taketa share Adawiya daƙin yin komai game da ɗan gyarata yasa Umm ta maidota sashenta. Gyaran da bazai cutar da itaba ta shiga mata. Musamman fatarta da kuma maganin sanyi. da koya mata dabarun zaman aure. Ɓangaren girki da aikin gidan tasan bata da matsala, tunda su duka tsaye suke akan yaransu ta wannan fanin duk da kowane sashe akwai ƴan aiki. Dan danan cikin sati guda ta canja tai fes abunta. Idan tana ɗaki ita kaɗai tata kallon kanta a mirror kenan tana tiƙar rawa da gwada yanda zata kasance da Yah Abdallah. Duk da kuwa a yanzu ko kallo basu ishesaba daga ita har Yusrahn. Ko yarda ya haɗu da suma bayayi sam, idanko yaga ɗaya daga cikinsu a waje yata fama haɗe fuska kenan tamkar an aiko masa da saƙon mutuwarsa. Hakan bai dametaba, dan tasan lokaci zaizo da sauyi wataran, kamar yanda a yanzu yazo da shi a garesu suka kasance matansa batare da mafarkinsu ya taɓa hasaso musu hakanba.       Tana tsananin takaici a ranta na haɗata da Yusrah da akayi matsayin matansa, amma ta wani ɓangaren hakan bai damunta, musamman da akace itace zata fara binsa, ta barma kanta yanda sauran aikinta zai kasance tsakaninta da kishiyar tata (😖Adawiya!!!!!💣).           Yusrah kam dai tana cikin damuwa sosai. kullum cikin kuka take da roƙon Abbanta a warware auren ita bataso. Sai dai kowa yaƙi saurarenta, Amminta ce dai take tayata kuka dan tasan da gaske Yusrah bataso ɗin. Amma yaya zasuyi da ƙaddara?.         A washe garin da aka cika kwanaki goma da faruwar al'amarine tafiyar Adawiya da Abdallah ta kama.       Umm da kanta ta samu Addah har ɗaki tai mata ƙorafi akan yanda take share Adawiya. Sai da ta nuna mata ɓacin ranta akan hakan sosai sannan ta ɗora da mata nasiha akan ta yarda da ƙaddara mana.         “Addah Minene laifin Adawiya tunda ba itace ta saka a ɗaura mata aure da Abdallah ba. Ba kuma itace tabama Nu'aymah shawarar ta gudu ba. A ganina addu'a ya kamata mubi yarannan da shi tare da fatan alkairi bawai tsangwama da hantara ba dan su basu da laifi”.         “Umm bazaki ganeba wlhy, ke dai kibar......”       “Naji bazan ganeba Addah”. Umm ta dakatar da Addah da sauri. Ta cigaba da kallonta tana faɗin, “Baki da wani abinda zaki faɗamin da zaki kare kanki, ni dai kawai ki dawo rayuwa da yaran nan kamar yanda kikeyi da. Ki kuma yima Adawiya fatan alkairi kodan sabuwar rayuwar da zata fuskanta a yau dan girman ALLAH”.       Shiru Addah tai tana sake jinjina ƙyawun zuciya irin na Umm, haka take ita komai tana ɗaukarsa da sauƙi a rayuwarta bata zafafama kanta. Tunda abinnan ya faru babu wanda ya taɓajin furucinta kosau ɗaya akai. Ko a fuska ƙoƙarin ɓoye damuwarta takeyi. Tausayin aminiyar tata kuma ƴar uwarta sai ya sake kamata fiye da da can.      Umm da kanta ta fita taje ta shigo da Adawiya, zaunar da ita tai kusa da Addah itama ta zauna. Su biyu suka shiga yima Adawiya nasiha kamar yanda sukeyi a duka sauran ƴaƴan Addah uku da aka aurar. Sumayya, Maryam, Badariyya. Sai da sukai mata nasiha sosai kafin Umm ta tashi ta fita ta bar Adawiya da Addahn.  ★★★★         Kamar yanda tsari da al'adan mutanen gidan yake bayan sallar la'asar iyayen suka sake haɗuwa aka rufu kan Adawiya da Abdallah akai musu faɗa da nasiha sosai. Tare da gindaya musu sharuɗa masu tsauri akan duk wanda wani al'amari mara ƙyau ya ɓullo daga wajensa a cikinsu to lallai zai fuskanci ɓacin rai da fushinsu sosai. Daga ƙarshe aka sake musu doguwar addu'a aka sallami Adawiya da ko sau ɗaya batai hawayeba da iyayensu mata.      Umm ta tafi da Adawiya sashenta danta kimtsata, suka bar Abdallah tare dasu Baba Malam da Hajjo da suka sake ɗora masa da Nasiha kasancewarsa shine babba.         Ƙarfe 7:30pm gayyar yaran gidan harna ma'auri su Aysha sukaima Abdallah da Adawiya rakkiya airport dan jirgin 8:30 zasu bi zuwa ƙasar Dubai. Sai sunyi kwanaki goma acan kamar yanda Abdallah ya tsarayi da Nu'aymah sannan su wuce Saudia.        A yanzuma dai idanun Adawiya ƙifi-ƙifi babu ko ɗigon hawaye a cikinsu. Hakan ba ƙaramin ƙona ran Addah yayiba. Hakama Momyn Abdallah al'amarin ya bata tsoro, taita kallon Adawiyar cike da alamomin tambaya a ranta, sai dai bata furtaba.             Ko kaɗan Yusrah bataji komai a rantaba, dan ko kusa bata kawo Adawiya ma a cikin matsalolinta saɓanin Adawiyar dake jin zafin Yusrah babu gaira babu sabar. Ita Yusrah dama za'a warware nata auren da tayi matuƙar farin ciki. Amma ta ɗauka alwashin cigaba da addu'oi tana gayama ALLAH kukanta akan hakan kafin lokacin da akace zata tare.       Basufi zaman mintuna talati da huɗu ba aka sanar da tafiyarsu. Sai yanzune Adawiya taɗanji babu daɗi a cikin ranta na kewar ƴan uwanta. Amma saita fuske ta shiga binsu ɗai-ɗai tana rungumarsu. Da tazo kan Yusrah saita wuce batace mata komaiba. Ba ƙaramin mamaki hakan ya bama kowaba, duk suka bita da kallo har Yah Abdallahn. Tsarguwa da tai ne ganin yanda ƴan uwan nata ke binta da kallon tuhuma ya sakata buɗe jakkarta ta ɗakko wani abu ta nufi Yusrah, hannunta ta kama ta saka mata abin sannan ta rungumeta kamar yanda taima kowa.       A kusan tare duk suka sauke ajiyar zuciya, dan da da yawansu abun yay musu cak a ƙirji hatta da ƴan uwanta da suka fito ciki ɗaya. Musamman Hajarah da taga abinda ya faru a ranar ɗaurin auren tsakanin Addah da Adawiyan.      Sallama suka sakeyi da juna. Kafin tabi bayan Yah Abdallah da yay gaba abinsa batare da ya saurareta sun jera tareba kamar yanda taso. “Hummm!! Wasa farin girki Adawiya👁👎🏻”. ___________________ NU'AYMAH ______________               Tun randa aka barota daga gida bata sake sanin halin da take a ciki ba sai washe gari da yamma. Farkawa tai a tsananin firgice. Sai dai nauyin masifa da kanta yay mata na azabar ciwo ya sakata sakin ƴar siririyar ƙara da dafe kan nata da hannu bibbiyu tana sakin numfashi a wahale.         Sake ƙoƙarin buɗe idanunta tai da ƙyar saboda nauyin da sukai mata suma. Tabi ɗakin da take ciki da kallo mai ƙaracin haske, sai dai ba dunɗum yakeba. Katifa ce kawai a ɗaki da wasu lalatattun akwatuna guda uku kalar ruwan ƙasa. Sai takalma na maza da aka jera a gefe kusan ƙafa shidda. Sai hanger a jikin bango anyi hanging farar jallabiya ta maza guda ɗaya da wanduna uku duk baƙaƙe. Sake lumshe idanunta tai ta buɗe a hankali dabin jikinta da kallo.      Hijjabin tane dai a jikinta har ƙasa da ta saka lokacin da zata fita neman wayarta. Ta kai hannu da ƙyar ta laluba jikinta. Towel taji wanda shima shine tasan ta ɗaura a jiyan, sai dai yanzu ya kwance duk ya zazzame daga ƙirjinta ya dawo saman cikinta.       Juya mata da garin ya farayine ya sakata yin baya ta sake kwanciya a katifar hawaye masu a zabar zafi na silalo mata a saman kumatu. A haka ta cigaba da kwanciya tana zirarar da hawayen jikinta duk babu wani ƙarfi. Tafi mintuna talatin da kwantawa sannan aka buɗe ƙofar.     Kasa buɗe idanu tai balle taga wanene ya shigo ɗin, tsahon mintuna biyar kafin ta buɗe idon kaɗan ta saukesu akan wanda ke tsaye jikin ƙofa sanye da baƙaƙen kaya, hatta da hannunsa akwai safar hannu baƙake. Hakama fuskarsa da facemask, idanunsa kawai take iya gani. Suma ganin kallon da take masa ya sashi ciro glasess ya toshesu.     Basket ɗin dake riƙe a hannunsa ya tako gaban katifar ya ajiye batare da yace da ita uffanba ya juya ya fita. Maida idanunta tai da ƙarfi ta rumtse zuciyarta na zafi. Kukanma yanzu sai ya kasa fita mata. Haka ta cigaba da zama a wajen har bayan mintuna kusan goma da fitarsa. Sai kuma ga mace ta shigo sanye cikin dogon hijjab har ƙasa. Itama fuskarta sanye take da niƙaf.      Batare da tama Nu'aymah magana ba ta kamata ta tayar. Bata da wani ƙarfi ko iya yin magana, dan haka ta cigaba da bin matar kawai a yanda taso. Ƙofa ƙwara ɗaya ƙarama dake a cikin ɗakin suka nufa, sai da suka shiga Nu'aymah ta fahimci toilet ne. Fas yake babu ƙazanta a cikinsa, saima ƙamshin omo da hypo daketa tashi.       “Kiyi wanka”. Matar ta faɗa a taƙaice batare da ta jira amsar Nu'aymah ba ta fice abinta. Da kallo kawai Nu'aymah ta bita, sai dai bakinta ya mata nauyi ta gaza cewa uffan a yanzunma. Kamar bazatai wankanba sai kuma wani tunanin yazo mata. Rabonta da salla tun ta isha'in jiya. Ga shi a yanzu da alama har anyi sallar la'asar ma. Tana buƙatar ƙarfin jiki sosai, hakan kuma bazai yuwuba sai tayi wankan.      Cikin ƙarfin hali ta zare dogon hijjabinta da towel ɗin, duk da tsaftar banɗakin a ɗarare tai wankan. Taji ƙarfin jikinta sosai, sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi a jajjere. Alwala tayi ta fito tana daddafa bango, dan akwai yunwa tattare da ita.      Da mamaki ta kalli kayanta da aka ɗaura a saman katifar, ta bi ɗakin da kallo kamar ɗazun, babu kowa sai kayan a ajiye da kuma kwanikan abincin dake cikin basket ɗin suma an fiddosu ƙasa an ajiye.         Bata da wani zaɓin daya wuce canja kayan tai sallolin dake kanta. Harta kammala rama sallolin babu wanda ya sake shigowa, ta kwanta saman abin sallar tana hawaye da tunanin ko wane hali yanzu Umm da Abbanta da Muh'd dama duka sauran ƴan gidansu suke ciki a yanzu na rashin ganinta?. Yah Abdallahn ta, tasan zaifi kowa shiga tashin hankali bayan Umm da Abbanta. ‘Minayi suka kawoni nan? Su wanene su? A ina nake?’. Ta faɗa a fili tana sake fashewa da kuka. Taja tsahon lokaci tana ribzar kukanta, har kanta yana masifar sara mata fiyema da ɗazun. Barcine ya fara figarta na wahala. Jin motsin shigowar mutum ya sakata tashi zaune zumbur. Matar ɗazunce, yanzuma batai mata magana ba ta ɗakko kwanikan abincin ta kawo gabanta da mata alamar taci.       Yunwa Nu'aymah takeji sosai, dan haka batai musu ba taja abincin tahau cinsa. Taci sosai har matar tai mamakin hakan. Matar ta miƙe zata fara tattare kwanikan Nu'aymah ta kalleta cike da rashin tsoro tace,        “Su wanene ku? Miyasa kuka kawoni nan? Minai muku kuma?”.      Kallonta matar tayi sosai, amma sai batace da ita komaiba ta tattara kwanikan tai ficewarta.         Tashi Nu'aymah tayi ta nufi ƙofar da sauri, sai dai tana taɓawa tajita a kulle, fashewa tai da kuka ta koma saman katifar ta sake kwanciya tana sambatun kiran Umm da Abbanta da Yah Abdallah.         Tun daga wannan ranar kullum hakan ta cigaba da faruwa, zasu kawo mata abinci sau uku a rana, matarnan zatazo ta gyara ɗakin ta wanke mata bayi da kayan data cire. Sannan ta haɗa mata ruwan wanka ta sakata cin abinci. Tambayar duniya tai mata bama bata amsa, haka shima namijin idan zai shigo sau goma tai masa magana baya ko mata tari. Iya kacinsa ya leƙo ya ganta ya koma.      Haka Nu'aymah ta cinye kwanaki goman nan cikin matsanancin damuwa da tashin hankali. Babbar damuwarta halin da ahalinta zasu shiga na rashinta. Musamman ma Umm ɗinta da Abbanta da Yah Abdallah da Hajjo. Tayi kuka harta gaji ta bari ta koma gayama UBANGIJI kukanta. Dan tasan shine mai rahama mai jinƙai. Ya fita sanin dalilin da yasa ya jarabceta da wannan al'amari a daren ɗaurin aurenta da yayanta masoyinta.        Ranar data cika sati biyu a ɗakin bayan sallar la'asar sai ga matar nan, kamar kullum yauma batai mata magana ba, saima kwashe kayanta data cire tai ta fita dasu. Bayan kamar mintuna goma sai gata ta dawo ɗauke da hijjabi wankakke gogagge. Miƙama Nu'aymah tai da mata alamar ta sanya. Babu musu Nu'aymah ta fisgi hijjabin daga hannunta tana watsa mata harara ta sanya. Ita sam bata wani jin tsoronsu, damuwarta kawai family nata.       Matar bata kulataba, bayan ta saka hijjab ɗin ta zagaya ta bayanta ta riƙe mata hannaye. Fisgewa Nu'aymah ta fara ƙoƙarin yi amma ta kasa saboda ɗaure hannayen da matar tayi. Kafin ta samu damar magana namijin ya shigo shima. Gaban Nu'aymah yaje ya tsaya tare da fiddo baƙin ƙyalle a aljihunsa ya ɗaure mata idanu.      Duk tsiwar da take masa bai kulataba balle ya tanka. A haka suka fita da ita a ɗakin batare da tasan ina za'a kaitaba.............✍ _____________________ SAHFAT PREORDER! ______________________         Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗. SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya. Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske. *_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._* _To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_. Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU. Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa. *_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_* _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* No. 7 ................Sosai gazawar Umm take ƙoƙarin bayyana ga kowa. Dan gaba ɗaya yinin yau da Nu'aymah ta yisa a ranta. Tun tana kukan zuci kamar yanda ta saba har hawaye suka kai ga fara sakko mata daga idanu.         Wajen misalin biyu da rabi na rana Baba malam ya shigo gidan. Kamar yanda al'adarsa take inhar ya dawo daga wajen aiki sai ya fara zuwa sashen Hajjo yaga lafiyarta. yauma haka ne. Zaune ya isketa a falo Imran na tausa masa ƙafa yana kumbura baki dan ta sakashine dole.      Murmushi Baba malam yay da zama a ƙasa gefenta kaɗan da ajiye mata ledan kayan fruits idonsa akan Imran ɗin da shi sam hankalinsa bai kai kansa ba.            “Imran ya naga fuskar a kumbure? Ko dai aikin innah ne ba'a son yi?”.      Kallonsa Imran yay da sauri, sai kuma ya saki ƙafar Hajjo ya nufi baba malam ɗin yana sake tunzura baki gaba. “Baba sannu da dawowa”. Kafin Baba malam ya bashi amsa Hajjo ta katsesa. “Dan gidanku dawo ka cigaba, inba hakaba kasan ALLAH nasan ta inda zan rama mai ƙwalelen ƙeya kawai”.       Dariya Baba malam yayi yana kallon yanda Imran ɗin ya cika yay fam, sai kuma ya kalli Hajjo da itama ta kumbura farar fuskarta da duk tai tamojin tsufa tana zubama Imran ɗin harara......        “Ni wlhy na gaji Hajjo, kumafa Momy jirana take zan mata aika”.      “Oh! Uwarka ta fini kenan?..” Baba malam yay saurin haɗiye dariyarsa da matsawa kusa da ita gab ya kama ƙafar tata ya aza saman ƙaramin filon kujera. “Kinga Inna manta da shi kinji, idan shima yana tsoron ɓatama mamarsa nima ai gani tare dake ko?”.          Murmushi tayi kamar ba itace da fuska a kumbure ba. Sai kuma ta watsama Imran ɗin harara tana faɗin, “Tashi ka fitarmin a falo to kirikun banza, indai nice ai inada ranata yaro”.      Tashi Imran yay da sauri dan ganin Hajjo ta kwakuso filon kujera da alama dukansa zatayi. Sai da yaje bakin ƙofa sannan ya juyo. “Ai dai gobe idan ALLAH ya kaimu zamuyi komawarmu Abuja.......”      Kafin ya rufe baki ta tilla masa filon, kwasa yay da gudu ya fice yana ƙyalƙyala mata dariya.         “Wlhy Ɗan malam ƴaƴanku sun fetsare musamman ma ƙarshe-ƙarshen nan. Kaga akace maka Imran da Muhammadu da Jafar sunfi kowa rainanima a gidannan”. Hajjo ta faɗa a ƙufule.       Cike da girmamawa da lallashi baba malam yace, “To kiyi haƙuri inna zan musu faɗa kinji, yanzu dai ƙafar ciwo take miki ne?”.         “Kaɗan take ciwon dai, na neman man zafin daka siyomin shekaranjiya na rasa inda yake, na tabbata cikin ƴaƴanku wani ya ɗaukesa. Ƙilama Zainabu c.......” sai kuma tai shiru ta kasa ƙarasawa saboda tunawa da tai Nu'aymah ma bata gidan. To ita kaɗaice ke mata yanda ta gadama a cikin jikokinta a zauna lafiya a gidan. Dan suna mugun ɗasawa da Nu'aymah saboda duk aikin da ta sakata yimatashi take. Hatta da wanki Nu'aymah ce kema Hajjo. Hakama gyaran sashenta. Sai ko Adawiya itama sunaɗan shiri, amma ƙa'ida kullum sai sunyi faɗa.       Ɗan murmushi baba malam yayi mai ciwo, dan shima a kullum ɗiyar tasa tana a ransa. Ya sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Karki damu innah insha ALLAH zansaka Abubakar ya saya miki idan zai baro company. Sannan zanma Doctor Kabir magana yazo ya duba ƙafar, idan kuma asibitin zamu koma to”.       Jikinta a sanyaye ta ɗaga masa kanta, harya miƙe bata iya sake cemasa komaiba. Sai da yaje gab da fita sannan ta kira sunansa. “Ɗan malam!”. Juyowa yay da sauri yana ƙoƙarin haɗiye abinda ya tokare masa maƙoshi da amsawa da “Na'am Innah”.          “Har yanzu babu labarin Zainabu dai ko?”.      Murmushin yaƙe yay mata wanda yafi kuka ciwo, ya ɗan girgiza mata kansa da faɗin, “Innah tasan inda taje ta ɓoye kanta ai. Randa ta buƙaci ganinmu da kanta zata nememu, ki kwantar da hankalinki wannan yabar damunki”.      Bata iya cewa dashi komaiba yanzuma. Dan damuwa ƙarara ta hango a saman fuskarsa da cikin idanunsa. Amma dan ƙarfin hali sai yay mata murmushi sannan ya juya ya fita.           Tamkar wanda aka zarema lakar jiki haka ya isa sashensa. Da tsarabar da yayo ta fruits ya fara cin karo a falo alamar driver baiga kowaba ya ajiye a nan. Ya ɗanbi ledojin da kallo kafin ya ida shigewa cikin corridor ɗin da ɗakunan barcin su Umm suke. Kansa tsaye ɗakinta dake can ƙarshen dogon corridor ɗin ya nufa, yay sallama kusan uku a ƙofar ɗakin babu amsa, sai kawai ya tura ƙofar ya shiga da sallama.        Tsaye yay cak a ƙofar ɗakin riƙe da handle ɗin kofar yana kafe Umm dake zaune a saman gado, Muh'd na kwance ya aza kansa bisa cinyarta yana barci. Kan yaron take shafawa a hankali, kanta na kallon p.o.p idanunta na tsiyayar da hawaye.          Haɗiye tasa damuwar yay ya ƙarasa cikin ɗakin sosai. Harya zauna a bakin gadon kusa da Umm bata motsaba. Ya ɗaura hannunsa saman nata dake shafa na Muh'd. Nannauyan numfashi ta sauke da ɗago kanta. Kallon ido cikin ido sukaima juna ita da baba malam ɗin. Sai tai azamar saka hannunta na haggu ta share hawayen fuskar tata tana maye gurbinsa da murmushi.        “Sannu da zuwa Abban Nu'aymah. Yaushe ka shigo ban saniba? Gaba ɗaya na gajine shinefa nace bara nazo na.........” hannunsa yay saurin ɗorawa akan bakinta alamar tayi shiru. Yasan ba wani abune ya saka wannan kame-kamenba sai dogon gargaɗin daya gindaya mata akan karta sake masa maganar Nu'aymah koda da wasa ne. Umm macece ita mai biyyaya da gudun ɓacin ran mijinta, duk abinda ya nuna bai masaba ƙoƙarinta shine dainashi tai masa wanda zai sakashi a farin ciki koda ita zai cutar da tata zuciyar kuwa. Wannan yana ɗaya daga cikin abinda ya ƙara mata kima da daraja a gareshi, tare da sake girmama soyayyarta a ranshi.      Miƙewa yay ya ɗauki Muh'd a hankali ya matsar dashi can gefe ya kwantar. Ita dai tana binsa da kallone har ya dawo ya zauna kusa da ita sosai. Kamota yay ya kwantar da kanta a ƙirjinsa. A tare suka sauke nannauyar ajiyar juciya. Hawayen da taketa ƙoƙarin karsu zubo suka ziraro a guje suna sauka bisa jikinsa.         Idanunsa ya lumshe tare da sake kwantar da ita jikin nasa da ƙyau, ya zame ɗan kwalinta yana shafa kanta dake cike da gashi dogo mai yarfin furfura ɗai-ɗai alamar girma ya fara kamata. Sake kwanciya tai sosai da cigaba da hawayenta.     Sunja tsahon lokaci a haka har saida akai kiran sallar la'asar sannan. Itace ta ɗagashi da sauri. Hakan yasa ya farka daga barcin daya figesa shima. Tunda abinnan ya faru bai sake yarda sun kwana ɗaki ɗayaba tun randa ta kwana babu lafiya. Hakan yasa suke tsananin kewar ɗumin junansu. Matsar da fuskarsa yay gab da tata ya sumbaci goshinta da dogon hancinta.      Ɗan murmushi tamasa da sadda kanta a ƙasa na alamar jin kunya. Shima yay murmushin yana sauke ƙafafunsa ƙasa. Batare da yace mata komaiba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “Ki tada Muh'd yay alwala mu wuce massallaci”.        “To” ta amsa masa tana binsa da kallo. __________________________________               Ana shiga sallar la'asar jar motar na shigowa cikin layin. Parking yay a ƙofar ƙaton gate ɗin gidan yana kallon gate ɗin massallaci. Kafin kuma ya maido dubansa kan Nu'aymah dake a gefensa hannu da idanunta da baki a rufe tana gyangyaɗi.        Ɗauke kansa yay ya kashe motar gaba ɗaya. Bai fitaba, saima kwanciya yay jikin kujera ya lumshe idanunsa dake a cikin baƙin glasess ɗinsa.        Kusan mintuna uku da tsayuwarsu Nu'aymah ta farka. Sai dai kasancewar idanunta da bakinta a rufe suke sai bazaka fahimtaba. Addu'a kawai take jerawa a ranta na nema agajin UBANGIJI. Sai da aka fito massallaci mutane suka gama shashsharewa, sai hayaniyar yara ƴan islamiyya dake cikin harabar massallacin. Kusan biyar na yamma Baba malam ya fito daga cikin massallacin shi da wani maƙwafcinsu suna magana. Saurin tashi yay zaune da kallon Nu'aymah, yay azamar saka hannu ya ɗaye mata salataf ɗin da suka rufe mata baki da shi. Ƴar ƙarar azaba ta saki tana faɗin, “Mugu kawai, ALLAH zai sakamin”. Bai kulata ba ya kwance mata idanunta da hannunta suma. Wani irin farin cikine ya saukar mata a rai ganinta a ƙofar gidansu. Tana zumuɗin fita ya dakatar da ita.       “Malam ɗauki akwatinki ki wuce da shi”.      Juyiwa tai da sauri tana kallonsa batare da ta saki handle ɗin ƙofarba. “Bansan kallo, ki ɗau akwatinki nace”.           “Minene abin kallo a jikin naka banda baƙin hali da zalunci. Ni dai nasan banbar gidanmu da akwati ba mizaisa kuma na ɗauka na shiga da shi...”         “K!!!” ya daka mata tsawa a fusace. Hakan ya sakata dakatawa daga ƙoƙarin sake buɗe ƙofar ta juya tana watsa masa harara da manyan fararen idanunta masu yalwar gashi. “Minene namin tsawa malam?”. Maimakon ya bata amsa sai ya ɗaga mata yatsun hanunsa biyu dake a cikin safa yana faɗin, “Kinada zaɓi biyu. Koki ɗauka akwatin nan kokuma wlhy na maidake inda muka fito, kuma wannan tafiyar itace zata zamemiki ta har abada keda gida”.      Kafinma ya rufe baki ta miƙa hannu baya ta sungumi ƙaramin akwatinta ruwan hoda mai ƙyau. Batare data sake jira yace uffan ba ta buɗe murfin motar ta fice abinta.                    Sosai gaban baba malam ya faɗi, yabi Nu'aymah dake jan akwati zata shiga gida da kallo harta tura ƙofar ta shiga, kafin ya maido dubansa ga motar data ajiyeta. Akan idonsa mai motar yay reverse yabar anguwar.     Duk yanda yaso danne ransa suci gaba da magana da Alhaji Mani hakan ya gagara. sai kawai yay masa sallama akan yayi haƙuri anjima zasu ƙarasa maganar.        Da mamaki Alhaji Mani yabi baba malam da shi harya shige gida da kallo.. Ya ɗanyi shiru alamar tunani. Ganin bai hasaso komaiba sai kawai ya girgiza kai shima ya juya ya shiga nasa gidan da masallaci ya raba tsakaninsu da nasu Baba malam. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 __________________ __________________              Nu'aymah na isa tsakiyar gidan ta yadda akwatin ta kwasa da gudu zuwa ciki tana ƙwala kiran sunan Umm da Hajjo, dan gani takema tafiyar ɓata mata lokaci takeyi na isa garesu.         Ba Umm da Hajjo kaɗaiba kowa ma na gidan sai da ya fito, yaran ne kawai da suka wuce islamiyya babu. Samarinma yawancinsu sun dawo daga wajen aiki da makaranta ga waɗanda ke jami'a.          Wani irin tsalle Nu'aymah tai ta ɗane wuyan Umm dake tsaye a ƙofar sashenta tamkar wata gunki. Hakan yayi dai-dai da shigowar Baba malam gidan a matuƙar fusace.          “K!! Nu'aymah! K!! Nu'aymah kina ina?”. Baba malam dake shigowa tun daga gate ya fara kwala ma sunanta kira kamar zai haɗiye harshensa.        Da sauri Nu'aymah ta saki Umm jikinta na wani irin rawa, dan abin yazo mata a yanda batai zatonsa ba. Akwatinta dake yashe a ƙasa ya shura da ƙafa yana faɗin, “Zoki ɗauka ki koma inda kika fito kafin harshena ya furta miki abinda har ki ƙare rayuwarki zai zame miki musiba”.         Idanu sosai Nu'aymah ta zaro waje jikinta na sake ɗaukar tsuma. Muryarta na rawar fitar kuka tace, “Abba......” Katseta yay a tsawace yana nuna mata hanya da yatsansa.      Ba'ita mai laifin kawai ba, kowama yayi tsuru-tsuru a gidan hatta dasu Abba Rudwan sun kasa magana, dan sunsan ran yayan nasu a matuƙar ɓace yake. Hajjo ce kawai zata iya sakashi ko hanashi a irin wannan yanayin. Gashi kuma bata fitoba, ƙila wanka takeyi.         “Ba dake nake magana ba ne?!!”. Fashewa da kuka Nu'aymah tayi ta durƙushe ƙasa. “Abbah wajen waɗanda suka sacenin kakeson na koma?”. Tsaki yaja mai ƙarfi, dan yama ɗauka maganarta raini da iya shege.           “Lallai Nu'aymah kin girma! Ashe wayonki da iya tsara abubuwa har ya kai haka ƙarfi? Ki sanar mana kinbi saurayi saboda kar a aura miki Abdallah sannan ki dawo mana da wani sabon rainin wayon saceki akayi?. To idan saceki akayi uban wanene ya rubuta saƙwannin da kika barmana? Wanene kuma ya sacekin? Wanda naga ya ajiyeki yanzu shima wanene?. Duk sai ki bamu waɗanan amsoshin muna saurarenki?”.        Kai Nu'aymah ta shiga girgizawa tana hawaye. “Wlhy Abbah bansan komaiba akai. Bansan su wanene ba? Bansan wanene wanda ya ajiyeninba nima? Sannan ban ajiye saƙon komaiba ga kowa wlhy”.        “Nu'aymah!!!”. A tsananin tsawace baba malam ya kira sunanta. Sai da hantar cikin kowa ta kaɗa da tsawarsa. Itama tai baya ƙasa wanwar jikinta na ɓari na tsabagen tsorata. Dan bata taɓa ganin fushin mahaifinta irin hakaba duk da tasan yanada zuciya.            Nufarta yay tamkar wani mayunwacin zaki, sai famar huci yakeyi jikinsa na tsuma.       Da sauri Abban Abdallah da Abba Mustapha suka sha gabansa yana gab da isa ga Nu'aymahn. Kareta sukayi yanda bazai ko iya ganinta ba balle ya taɓata.          Sake ɓaci ransa yay, ya kallesu da jajayen idanunsa da ƙwalla suka taru a ciki. kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa, ya juya zai zagayesu ya damƙeta.       Caraf aka riƙe masa hannu. Dan haka ya tsaya cak batare da ya shiryaba. Hajjo data fito yanzun nan saboda tsawarsa da taji ta kalli hannunsa data riƙe da tana sake tamke fuska batare da tayi magana ba.         A take dukkanin jikinsa yay sanyi laƙwas, sai wata irin zufa data shiga tsatstsafo masa a goshi. Sun kai kusan mintuna biyar a haka ana kallon kallo tsakanin duka ƴan gidanma. yayinda Umm tunda Baba malam ya shigo ta sulale ta koma ciki tana hawaye.          Da idanu Hajjo tai masa magana da yaren da tun yana yaro ya haddace sa, kafin ta saki hannunsa a hankali ta nufi Nu'aymah dake durƙushe ƙasa tana kuka har yanzun. su Abbah zagaye da ita suma har yanzun suna bata kariya daga baba malam. Kamata hajjo tai ta miƙar da ita ta rungumeta a jikinta. Nu'aymah ta ƙanƙame Hajjo sosai tana jan numfashi da ƙyar. A hankali kuma sai idanunta suka fara lumshewa, kafin kowa ya farga tama sume.          Hajjo da taji ta mata nauyi tai ƙoƙarin ɗagota amma ta kasa. Gabantane ya faɗi tace, “Kai Mustapha zoku duba yarinyarnan kamarma bata da rai”.       Ai kafinma ta rufe baki sun kama Nu'aymah da hanzari. Yaraf tai baya jikin Abban Adawiya alamar dai da gaske bata numfashin. Sake tashi hankalin kowa yayi, duk sauranma suka matso suna ambaton Innalillahi....       Ɗaukarta Abban su Adawiya yay ya nufi sashen Hajjo sauran biye da shi. Yana kwantar da ita bisa kujera Ahmad na miƙo ruwa daya ciro a fridge. Amsa Abban su Abdallah yay ya zuba a hannu sannan ya shafama Nu'aymah a fuska. Ko motsi bataiba balle ai tunanin farfaɗowar ta. Sake tashi hankalinsu yayi. Ahmad da Malam ƙarami suka durƙusa da saurin kama ƙafafunta suna murzawa, suma su Abba hannayen Nu'aymah suketa faman murzawa. Amma abin tashin hankali ko motsi bataiba har lokacin.           A yanzu kam kowa ya fara tunanin ciwon Nu'aymahr ne ya motsa, dan haka Abba Musbahu da bai jima da shigowa gidanba yay saurin faɗin, “Inaga a kira Doctor ɗinta, kamarfa ciwontane ya motsa”.         Cikin kuka Hajjo tace, “Kirashi Musbahu, dan ALLAH ka kirashi da sauri. Innalillahi......... Zainabu karki mutu ki barmu kinji”. Kukan Hajjo ba ƙaramin sake ɗaga hankalinsu yayiba, matan ma sai faman share hawaye sukeyi.         Duk abinda ke faruwa akan idanun Baba malam ne dake tsaye a jikin daga ƙofar falon Hajjo yana kallonsu. Kallo ɗaya zakai masa ka fahimci yana cikin tsananin tashin hankali. Nu'aymah zuciyarsa ce, yana dannewa ne kawai, amma bazai yuwu ya bari son da yake mata ya hanashi hukuntata akan kuskurenta ba, dan yasan icce tun yana ɗanye ake tanƙwarashi, idan ya bushe karyewa yakeyi.       Sun cigaba da ƙoƙarin ganin ta farfaɗo kafin Doctor ya iso, sai dai fa ko motsi babu wani sashe na jikinta dake nuna alamar zaiyi ma...........✍       Tashin hankali😪, kumuje zuwa. _____________________ SAHFAT PREORDER! ______________________         Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗. SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya. Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske. *_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._* _To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_. Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU. Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa. *_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_* _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* No. 8 ...................Doctor na isowa aka maida Nu'aymah bedroom ɗin Hajjo. duk fita sukai suka bashi waje yay aikinsa yanda ya kamata. Sai Abubakar da aka bari kawai dan ya taimaka masa da wani abun idan ya buƙata.         Sunyi jigum-jigum a falon Hajjo, kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa wadda ALLAH kaɗai yasan minene a cikinta.        Juyawa baba malam yay a hankali ya fice daga sashen. Sashensu ya nufa dan sai yanzune hankalinsa ya kai ga rashin ganin Umm tare da su. Babu kowa a falon, ya nufi bedroom ɗinta canma babu kowa. Fitowa yay ya nufi nasa ɗakin ko tana can. Sai dai kuma nanma babu kowa. A ɗan ruɗe ya dawo ɗakin Muh'd. Muhammad ɗin kawai ya samu yana canja Uniform ɗin islamiyya dan yanzun suka taso. Baima gansaba, sai da yace, “Muhammad ina Umm ɗinku?”      Jiyowa Muhammad yay da sauri, fuskarsa da ɗan damuwa yace, “Abba nima ban gantaba, na shiga ko ina bata nan kuma yunwa nakeji”.        Shigowa sosai Baba malam yay cikin ɗakin idonsa akan Muhammad ɗin. “Yunwa kuma Muhammad? Bakaci abinciba ka fita ne?”.        “Abba lokacin nasha fura wajen Hajjo na ƙoshi, yanzu kuma zanci”.      Kama Hannunsa Baba malam yay suka fita kitchen da tsammanin zaiga Umm a can. Sai dai kuma mai aikinta kawai suka samu tana gyaran kayan miya. Cike da girmamawa ta gaida Baba Malam ɗin. Amsawa yay yana cirar tuffah dake cikin fruit tray ɗin da suke sakawa. Ƙarasawa yay wajen fanfo zai wanke Saude tai saurin faɗin, “Baba malam kawo a wanke”. Baiyi musu ba ya miƙa mata tuffa ɗin guda biyu daya ɗauka. Sake bin kitchen ɗin yay da kallo kafin yace, “Ina Jannat ɗin take na ganki ke kaɗai kina aiki?”.        Saude data wanko apple ta ɗaura a ƙaramin filet tace, “Nima na shigo ban gantaba, dama naje can ƙasan layine na sayo mata daddawa data bada. To nadawo kuma na duba kamar ta fita, shine nace bara na gyara ko kayan miya kafin ta dawo”. Shiru Baba malam yayi gabansa na faɗuwa. Amma sai ya danne ya kalli Muhammad dake saurarensu. Filet ɗin tuffa ɗin ya miƙa masa yana faɗin, “Karɓa wannan kaje kaci muje salla mu dawo saika zauna cin abincin”.          Kai Muhammad ya ɗaga masa da amsar filet ɗin. Yaron nagaba yana biye da shi har suka fice. Sake komawa yay ɗakin Umm ɗin dai zuciyarsa na bala'in harbawa. Tsaye ya isketa gaban Wadrobe tana fiddo kaya da alama wanka tayo. Ya sauke ajiyar zuciya da faɗin ‘Alhmdllh’ a fili. Hakanne yasata juyowa da sauri dan bataji shigowarsa ba. Kamar zatai magana sai kuma tai shiru tana kallonsa kawai.        “Naje massallaci”. ya faɗa a taƙaice yana juyawa ya fita daga ɗakin. Binsa da kallo Umm tayi harya ɓace mata sannan ta ɗauke kanta hawaye na ziraro mata. ★★★★         A ɓangaren Hajjo Doctor ya bama Nu'aymah dukkan taimakon daya dace kamar yanda ya saba a duk lokacin da ciwon nata ya motsa. Sai dai yau ta jima bata farfaɗo ba. Dan sai da sukaje sukai sallar magriba suka dawo sannan ya ƙarasa ƴan dabarunsa cikin amincin ALLAH ta farfaɗo.          Godiya yayma UBANGIJI tare da fita ya sanar musu ta farfaɗo. Dan yau ana idar da salla gaba ɗayansu suka baro massallaci, baba malam ne kawai yay zamansa. Matanma suna idar da sallar duk nan suka sake dawowa harda yaransu da dawowarsu islamiyya sukaji komai.       Bayan Doctor ya kammala komai ya buƙaci tattaunawa da su Abbah. Da ƙyar suka samu Baba malam ya baro massallaci yazo.         Doctor ya gyara zamansa cikin girmamawa a garesu yace, “Gaskiya wannan karon jikin Nu'aymah yayi tsamari. Kunsan matsalarta ba'aso abu yana firgitata da tsanani. tsawa da duhu suna gaba-gaba wajen girmama ciwonta da ƙarfafa shi”.         Hajjo ce tai saurin faɗin,  “Hakane likita, duk munsan wannan, kuma ana ƙoƙarin kiyayewa. Yau ɗinma kuskure aka samu kasan ajizanci na ɗan adam. Yanzu minene mafita?”.            “To Hajjo ALLAH ya kiyaye gaba, amma kam yau abin yaso yin tsamari sosai a gareta, dan yanzu haka zancen da nake muku sam bata cikin hayyacinta, fatanmu dai ta dawo hayyacinta lafiya batare data manta komaiba ma bayan ta farka”.        Da matsanancin tsoro suke kallonsa, sai dai kowa ya kasa magana. Da sauri yace, “Bamu da tabbacin hakan, komai na ALLAH ne, mucigaba da mata addu'a insha ALLAHU zata farko cikin ƙoshin lafiya. Dama inada shawara ne, dan tun kwanaki naso zuwa da zancen sai nai tafiya kuma, yau kwanana shidda kenan da dawowa ma, zan kuma iya komawa a koda yaushe dan na samu gurbin ƙaro karatu a ƙasar Australia ne”.         A tare sukace, Masha ALLAH, ALLAH ya sanya albarka ya bada ikon karanto abu mai amfani”.       “Amin ya rabbi, nagode sosai”.       Abbah Musbahu yace, “Muna surarenka. Wane shawarace da kai?”.         “Dama akwai wani likita babba kuma ƙwararre, dan kam ALLAH ya hore masa baiwa ta fannoni da dama inhar a ɓangaren likitancine. To wani abokina ya tabbatar min har masu irin ciwon Nu'aymah yana basu taimako. Matsalar ɗaya ce, shine ganinsa. Ganinsa nada matuƙar wahala dan yana aikine a Nigeria da wajen Nigeria. Ko a yau zai iya shigowa kano ya duba marasa lafiya ya fice, zuwa dare kuma kaji bama ya ƙasar gaba ɗaya”.             “To ai mu Doctor ko biyansa ya kama muyi sai muyi dan yazo ya duba ta”. Cewar Abban Abdallah.         “Ai anan gizo ke saƙar Malam. Dan ko nawa za'a biyashi bazaizo gida duba mara lafiya ba. Dolene sai dai mutum yaje yay tanadin ganinsa kamar kowa, zai baka date ɗin da zaka gansa idan har ciwonka yakai shi zai dubaka, idan kuma yaga akwai mafita zai haɗaka da wani likitan da zakaje ka gani. Date ɗin da za'a rubuta maka kuma dole a sannan ne zaka gansa babu alfarma. Kwanaki yaron president ya samu wata babbar matsalar da sai shine ake fatan ya dubasa ko za'a dace. Har jirgi aka aika ya ɗakkosa daga wata ƙasar dan kawai yazo ya dubashi amma yace suje su sai kati subi layi kamar yanda kowa keyi shi bazaije ba. Kuma dole hakan akayi”.       Babu wanda bai jinjina wannan al'amari ba a cikinsu, sukai shiru kowa na tunanin mafita kuma. Ganin haka Ahmad yace, “To Doctor idan babu damuwa ai muma sai kai mana hanya mubi hanyar data dace ɗin na ganin nasa kawai, ko'a ina yake mu zamu bisa insha ALLAH. Fatanmu dai a dace”.         “Hakan shine dai-dai. Ga Number ɗaya daga ma'aikatansa zan baku sai ku nemesa, insha ALLAH zai muku ƙarin bayanima fiye da nawa ma, ga kuma ta abokina ma duk zan haɗa muku shima likitane zaku iya neman taimakonsa koda ni na wuce ne”.       Rubutawa yay ya miƙama Hajjo dake a kusa da shi, ita kuma saita miƙama Baba malan da tun shigowarsa baiyi ko tari ba. Bai musaba ya amsa ya ajiye gefensa da nufin idan ya tashi sai ya ɗauka yaje ya adana. Doctor ya tattare file ɗin bayanan ciwon Nu'aymah waje guda ya sake miƙama Hajjo yana faɗin, “Da wannan zaku gansa dole, dan ƙa'idarsa sai yaga bayanan ciwon mutum na baya inhar ya taɓa ganin likita akan hakan”.      Nanma godiya suka sake masa. Hajjo ta sake miƙama baba malam. Amsa yay ya saka Numbers ɗin da aka bashi a cikin file ɗin ya ajiye.      Kasancewar lokacin sallar isha'i yayi duk sai suka fice har Doctor. Bayan an idar da salla Doctor ya sake dawowa tare dasu Ahmad ya shiga ya ƙara duba Nu'aymah. Sai da ya sake tabbatar da komai ya zauna sannan ya fito yay musu sallama akan insha ALLAH da sassafe zai dawo yaga jikin nata. Idan kuma sunga da wata matsala komai dare su kirashi.      Sun masa fatan alkairi da godiya ya tafi. _★__★_       Baba malam bai shigo gidan ba sai kusan goma saura, dan ya tsaya sunyi karatu ne. Sashen Hajjo ya fara shiga ya duba Nu'aymahn. Har sannan barci take, dan haka ya ɗauka file ɗin nata ya fice da shi zuwa sashensu.       Duk abinda Umm take masa bata fasaba. Yanda kuma bai mata magana akan Nu'aymahr ba itama batace da shi ƙala ba har suka kwanta. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 _______________________ WASHE GARI _______________           Alhmdllh Nu'aymah ta tashi jikinta da sauƙi, kuma kamar yanda kowa yay fata bata manta da komai ba kamar yanda Doctor yayta jin tsoro. Hajjo ce ta taimaka mata tayi wanka. Yusrah ta kawo mata abinci tama zauna da kanta ta ringa bata. Ta ɗanci babu laifi, dan Yusrah lallaɓata ta dingayi ita da Hajjo.      Kamar yanda kowa na gidan yazo ya dubata da safen haka Baba Malam da Umm ma sukazo suka dubatan. Sunji nutsuwa sosai a zukatansu ganin jikin nata Alhmdllh. Sai dai kowansu bai nunaba a fuska, sunma haɗe mata gabas da yamma.     Hakan ba ƙaramin sake ɗaga hankalin Nu'aymah yay ba, harta kasa haƙuri ta shiga tambayar Yusrah ko wani abu ya faru bayan barinta gida ne? Dan ita tayi zaton idan ta dawo zataga kowa na murnar dawowar tata. Amma saita samu saɓanin hakan, sai ma kalaman baba malam na jiya keta mata kaikawo a cikin rai.     Ƙasa Yusrah tayi da kanta hawaye na cika mata idanu, haka kawai ta tsinci kanta da jin kunyar Nu'aymah ɗin mai tsanani. “Yusrah dan ALLAH kimin bayani mana? Ina Yah Ab da Adawiya duk bamma gansu ba”. Nu'aymah tai maganar cikin sanyin murya na alamun rashin jin daɗin jiki.      Saurin miƙewa Yusrah tayi ta juya mata baya zata bar ɗakin. Nu'aymah ta riƙe hannunta itama da sauri. Hannu Yusrah tasa ta goge hawayen dake rige-rigen sakko mata a kumatu batare data juya ta kalli Nu'aymah ba.      Dai-dai nan Hajjo ta shigo tare da Doctor da yazo sake zuwa ganin jikin nata.          “Kai lafiyarku?”. Hajjo ta faɗa ganin Nu'aymah da Yusrah duk suna hawaye.          “Ba komai Hajjo”. Yusrah ta bama Hajjo amsa tana zare hannunta daga cikin na Nu'aymah. Kamar hajjo zata sake magana sai kuma tayi shiru suka bama Doctor damar duba Nu'aymahn. Yaji daɗin ganin jikin nata normal, sai dai yanason mata allura yana tsoron rikicinta da zasu kwasa. Nu'aymah ta mugun tsanar allura a rayuwarta, indai akace za'ai mata allura to lallai an taro match kuwa. Dan sai kowa yaji a gidan harma makwafta.      Kallon hajjo yay murya ƙasa-ƙasa yace, “Hajjo ko za'a kira mana su Ahmad ne kusa. Allura zan mata kinsan kuma sai ansha yaƙi”.        Sosai hajjo ta waro idanu waje. Taɗan kalli Nu'aymah data kwanta idonta na kallon fanka dake juyawa a hankali. Sake kallon Doctor tayi, itama a hankali tace, “bara dai a dubamin cikin iyayen nasu tunda duk basu fita ba”.     Kansa ya ɗaga mata ya tashi ya fita falon dan ya haɗa allurar. Itama Hajjo biyosa tayi.       Kusan mintuna biyar da fitar tasu duk suka dawo harda Baba malam dake cikin shirin fita. Batare da yayi maganaba ya kama Nu'aymah da kansa ya tayar zaune. Kallonsa take cike da so da ƙaunar mahaifin nata. Amma yanda yay kicin-kicin da fuska sai yake ƙara tsoratata. Ganin yanda ya jata jikinsa ya rungumene ya saka ƙirjinta bugawa. Dan tun tana yarinya inhar taga ya mata irin wannan rungumar to lallai allura za'a mata. Saurin ɗagowa tai ta kalli Doctor daya ɓoye hannunsa a baya. Jikinta ne ya fara tsuma, zatai magana Baba malam ya balla mata hararar da ta sakata maida kanta jikinsa ta kwantar.       Rikici sosai akasha kafin Doctor ya mata allurar, ba ita kanta ba har baba malam da hajjo masu riƙetan saida ta tarama gajiya. Doctor kam har ƴar zufar wahala yakeyi a goshi, a ransa yana sake jinjina daru irin na Nu'aymah.         Tunda baba malam ya maidata ya kwantar ajiyar zuciya kawai taketa faman saukewa hawaye na zirarar mata da gudu. Hajjo ta zauna inda baba malam ya tashi ta ɗago kan Nu'aymah ta aza bisa ƙafarta tana shafa mata dogon gashinta.        Sauran magungunanta Doctor ya ajiye yayma hajjo sallama suka fice shi da Baba malam.         Hajjo ta jima tana lallashin Nu'aymah kafin ta samu tayi shiru barci ya saceta. Amma har cikin barcin tsabar rikicinta ajiyar zuciya taketa faman saukewa a jajjere. Haka dai hajjo ta lallaɓa ta kwantar da ita da gyara mata kwanciya ta tashi ta fice. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 _______________________ ______________ DUBAI ________               Amarya Adawiya da ango Abdallah sun isa ƙasar dubai lafiya, sai dai gaba ɗaya ya canja tsarin daya shiryama kansa da Nu'aymah. Ya dai kama musu babban hotel kuma a ɗaki ɗaya. A randa suka isan kuma ya sace wayar Adawiya ya ɓoye batare data saniba.      Ita dai duk abinda yake mata bai ɓata mata rai, haɗe fuska da ƙin mata magana tunda suka taho baisa taji haushinsaba balle sonsa ya ragu mata a zuciya. Saima ƙaruwa da ya sakeyi tanajin kamar ta haɗiyesa.      Gadon ya bata ta kwanta shi kuma yasa bargo a ƙasa yay kwanciyarsa. Da asuba ya rigata tashi, yay wankansa yay shiri tsaf. Sai da ya kammala komai sannan ya tadata. Mamaki ya kamata matuƙa ganinsa cikin shirin fita, sai dai kuma babu fuskar tambayarsa.        Murya a shaƙe yace, “Duk abinda kike buƙata ki kira zasu kawo miki”. Daga haka bai sake tofa komaiba yay ficewarsa daga ɗakin yaja mata ƙofar. Ta jima zaune a wajen tamkar wata gunki har gari yay haske sosai kafin ta sakko jiki a sanyaye taje tayo alwala. Duk da hakan da yay mata babu daɗi sai bataji haushinsaba. Haushin Nu'aymah nema ya kamata, dan a ganinta zaman dataine cikin zuciyarsa yasa baya ganin kowa da gashin mutunci sai ita. Aiko ta ɗauki alwashin sai ya manta wata banza Nu'aymah a zuciyar tasa har abada balle kuma wata Yusrah da tasan bata a gabansa. “Hajiya Adawiya, ke dai kike kiɗanki kike kuma rawarki🤣😏”.                Haka ta yini ita kaɗai, daga kallo sai cin abinci da kwanciya. Gashi ta nema wayarta ta rasa, sai kawai tunaninta ya bata kota barta a gidane kokuma ta yaddata a jirgi Yah Abdallah ya ɗauke mata. Ta barsa akan idan ya dawo zata tambayesa.          Abdallah bai dawo hotel ɗinba sai kusan 11 na dare, harkokin kasuwancinsa ya yini yi hankalinsa kwance. Baiyi zaton iske Adawiya ido biyu ba. Amma a mamakinsa sai ya sameta zaune dirshen tana kallo. Sannu da zuwan data masa kawai ya amsa ya ɗauke kansa. Ya ɗauka kayan barci ya nufi bathroom. Tana nan zaune ya fito tsaf da shi. Nanma bata ishesa ko kalloba ya zauna a ɗaya daga rukunin kujerun ɗakin yay kira a kawo masa tea. Babu jimawa akai knocking ƙofar. Adawiya ta miƙe jiki na ɓari zataje ta buɗe ya ɗaga mata hannu. Da kansa ya tashi yaje ya amso ya dawo yay zaman sha bayan ya kunna laptop.        Sunja tsahon lokaci zaune, Adawiya nata faman kallonsa kamar ta samu television, shiko aikinsa yakeyi tamkarma ya manta da ita a cikin ɗakin.       “Uhhm Yah Ab dan ALLAH ko kaga wayata?”. Cak ya tsaya daga aikin da yake yana sake tsuke fuska batare da ya kalleta ba. Ba komai ya jawo hakanba sai Yah Ab datai kiransa da shi. Dan Nu'aymah itace ta fara kiransa da suna har kowama ya ɗauka. itace kuma ke kiransa hakan a koda yaushe. Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Ya girgiza mata kansa kawai ya cigaba da abinda yakeyi. ★★★★         Haka suka cigaba da tafiya a kwanakin da duk suka gabata na barinsu ƙasarsu. Adawiya duk a takure take, dan Abdallah kullum da sassafe yake fita, bazai dawoba kuma sai sha ɗaya. amma soyayya ta rufe mata idanu ta kasa jin zafin hakan da yake mata.      Shiko gaba ɗaya ya ɗauketa yasa a kwandon shara ya maida hankalinsa ga kasuwancinsa kawai, dan a maimakon kwana goma da ya shirya yi a ƙasar ya maidashi kwana shida zasu wuce.          Tun a randa Nu'aymah ta dawo gida yay mafarkin hakan da daddare, aiko tunda asuba yay kiran Number Ahmad. Cike da farin ciki Ahmad ɗin ya sanar masa komai, dan dama shima yana da shirin kiran nasa, so yake kawai jikin Nu'aymah aga yanda zai kasance a washe garin.             Karan farko da tun faruwar al'amarin nan Abdallah yay sassanyan murmushi hawayen farin ciki na cika masa ido. Jiyake tamkar an tsundumasa aljanna yau. Yana katse kiran ya kira Momy itama. A lokacin dawowarta kenan daga sashen hajjo taje ta duba Nu'aymah itama.         Bayan sun gaisa cike da so da ƙaunar juna irin ta ɗa da uwa, ya tambayi lafiyar kowa a gidan sannan cike da zumuɗi yace, “Momy ashe Nu'aymah ta dawo?”.        Jimm tayi kamar bazata amsa masaba, sai kuma tace, “Uhmm! ta dawo jiya”.         “Kai Alhmdllhi Momy, yanzu zanje na saya mana tickets kuwa mu dawo, in ALLAH ya yarda wannan karon bazan sake ta sake kuɓuce minba Momy, a yau ɗin nan ina durowa koda magriba ne sai an ɗaura mana aur......”          “Kai! Shashasha dakata min. To idanma mafarki kake maza ka farka ka dawo hayyacinka. Wai kai Abdallah wane irin sakaran banzane halan? Ka fita idanuna tunkan na rufesu da kai a ciki wlhy. Bara makaji na maka mai kankat. Wlhy tallahi idan naga ƙafarka a ƙasarnan batare da ni nace kazoba ALLAH ya isa ban yafe maka ba.....”          “Momy!!” ya faɗa cikin tsananin tashin hankali.      “Yes! Abinda kaji shi na faɗa. Idan zakai haƙuri da waɗanda aka baka kayi. Hauka akeyi da za'a manna maka mata har uku ƴan family ɗaya uban ƴan son zuminci? Itama Yusrahn ina nan ina nema maka hanyar barinta wlhy. Adawiyar dai ta tsira tunda ALLAH ya sota ka baro ƙasar da ita da wuri. Idan suma sunada nasu zaɓin nima inada nawa ai, amma aka nunamin fin ƙarfi da ƴan uwantaka. Kai kuma shashasha da yake baka kishina hakan ko damunka bayayi. To wlhy kama cire wannan tunanin a ranka. Kuma ko a waya ka kira wani cikin iyayenku kace a ɗaura maka aure da Nu'aymah shima ban yafe makaba. Idan wannan maganar tasa ka kirani karka sake kirana”.     Ta katse wayar batare da ta jira cewarsa ba.       Sosai jikin Abdallah ke tsuma. Haƙoransa har wani bada sautin ƙara suke saboda rawar da bakinsa keyi. So yake ya faɗi sunan Momy amma ya kasa haɗa kalmar waje guda dan tsabar rikicewar da yayi.       “Yah Ab lafiya kuwa?”. Adawiya ta faɗa tana ɗaura hanunta saman kafaɗarsa. A fusace ya ɗago ya hankaɗe hannun nata tai taga-taga ta faɗa saman kujera. Ko kallonta baiyiba yay wurgi da wayarsa ya nufi bathroom da sassarfa. Yana shiga ya sakarma kansa shawa ruwan na saukar masa a jiki batare da ya cire kayaba.      Kalmar ALLAH ya isar Momy ce keta masa kai kawo a zuciya har kana hango sama da ƙasan da ƙirjinsa keyi na.        Adawiya kam tana ganin ya shige ta miƙe idanunta cike da hawaye. Da ƙyar ta ɗangyasa ƙafarta data buge da centre table ta isa inda yay wurgi da wayarsa. Addu'a take ALLAH yasa babu lock. Cikin sa'a kuwa babun, sai dai hoton data fara cin karo da shi a fuskar wayar ne yasata jin wani irin zafi tamkar an soki zuciyarta da mashi.        Hoton Nu'aymah ne da sukayi ranar walimar gama makarantarsu. Tayi masifar ƙyau a hoton, dan ɓakar doguwar rigar data saka na Material ɗinkin yay masifar zama mata a farar fatarta. Ga idanun nan sun bala'in fitowa cikin kwalli har wani ƙyalli suke saboda haske. Tayi ɗan murmushinta loɓar kuncinta data gemunta ta fito raɗam. Sosai Adawiya ke faman taunar lips da ƙarfi tamkar zata hudasu, duk da tasan hoton tunkan shi Abdallah ma ya gani hakan bai hanata jin zafi mai tsanani ba. Da kyar ta iya danne ranta ta shiga dan son ganin dawa yay waya. A fili tace, ‘Momy!. To mita gaya masa daya fusatashi haka har yake neman karya ni a banza?’. Bata da mai bata wannan amsar, gashi kuma batasan inda wayarta takeba balle ta kira wani ta tambaya. Tanajin tsoron yin amfani da tasa kuma yazo ya kamata. Da sauri ta ajiye wayar inda ya jefar jin za'a buɗe ƙofar bayin.        Tsaye yay cak a ƙofar bayin yana binta da kallon tuhuma fusatar zuciyarsa na daɗa bayyana saman fuskarsa.............✍            Kuyi haƙuri, jiya man kaina ne ya tsiyaye tas yasin na kasa typing😖. _____________________ SAHFAT PREORDER! ______________________         Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗. SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya. Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske. *_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._* _To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_. Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU. Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa. *_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_* _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* No. 9 .................Sosai Adawiya ta tsorata da mugun kallon da Abdallah ke jifanta da shi. Jan jikinta ta farayi baya a hankali ganin ya fara takowa yana nufota. “Y...y..Yah Ab wlhy babu abinda nayi da wayarka, Please dan ALLAH karka dak......”      Ta kasa ƙarasawa saboda kiran wayar da akayi. Shima cak ya tsaya daga bin nata yana kallon wayar. (Sweet Momy) ya hango ɓaro-ɓaro yana yawo akan fuskar wayar kamar yanda yay saving. Iska mai zafi ya busar daga bakinsa yana lumshe idonu. Tsinkewa wayar tayi aka sake kira. Yanda bai motsaba haka ma Adawiya ta kasa motsawa. Kallon wayar take kawai daga nesa tamkar yanda yake kallonta shima. Sai ka ɗauka gamo sukai da bomb.       Sai da Momy ta jera ma Abdallah kira har biyar bai ɗaga ko guda ɗaya ba a ciki. Daga ƙarshema saiya nufi wayar a fusace ya takata da ƙafarsa. A take screen ɗin ya shiga bada sautin fashewa.         Baya Adawiya tai da sauri tana mugun waro idanu da buɗe bakin mamaki. Al'amarin bai ƙara firgitataba sai da taga ya ɗauka wayar ya zare sim card ɗin ya karyashi biyu. ya kuma nufi toilet ya jefashi yay flushing a take.      Da sauri Adawiya ta koma inda take da ta tsaya zuciyarta na mata wani masifar bugu, ga wani irin tsoron Abdallah daya sake shigarta mai ƙarfi. Sam batai tunanin yanada zuciya irin hakaba. Duk da tasan ƴan gidansu kowa yanada wannan shegen zuciyar amma tazata tashi mai sauƙice ganin yanda bata cika ganin fushinsa ba. Ta gabanta yazo ya fice ko kallon inda take bai sake yi ba. Ya bugo mata ƙofar da ƙarfi har saida ta zabura jikinta na karkarwa........ *_NIGERIA_*              Cike da mamaki Momy ke kallon wayar tata tamkar idanunta zasu zubo ƙasa. A ranta take raya ‘To miya samu wayar Abdallah? Ta shiga bai ɗagaba, daga ƙarshema wayar ta jita a kashe’.        “Momy lafiya?”. Omar daya shigo falon ya faɗa idanunsa akan Momy dake tsaye tana ta faman juya waya.      Saurin ɗagowa tai ta kallesa, sai kuma cikin sanyin murya tace, “Omar yayanku ne wlhy, ya kirani bana kusa inaga ko cikin su Amal wani ya ɗaga, shine yanzu dana fito naga alamar ya kira an ɗaga saina kirashi. Amma har missed calls biyar na jera masa bai ɗaga minba, yanzu daga ƙarshema wayar a kashe take”.         Murmushi Omar yayi yana zama da faɗin, “Oh Momy ƙila to baya kusa ne, kinsan hidimar Yah Abdallah ba ƙarewa takeba. Nasan zai kiraki shima”.        Kai Momy ta girgiza masa, “Omar ba rashin ɗaga kiran bane damuwata, jin wayar a kashe bayan kuma duka kiran danai sun shiga”.        “Momy Please ki kwantar da hankalinki, nasan insha ALLAH babu wata damuwa. Koma baida cajine kokuma network”.     Kamar zata sake magana sai kuma tai shiru taɗan jinjina kanta. Tashi tai ta maida wayar a caji dan fama cajin ta saka ta shiga kitchen tun ɗazun. Yanzuma tana maida wayar a caji saita koma kitchen ɗin suka cigaba da aiki ita da masu aikinta su biyu tabar Omar daya kwanta cikin kujera yana canja chennal a falon. Sai dai kuma abin yaƙi barin ranta sam.         Har dare Momy na jiran kiran Abdallah shiru, ta kuma sake nemansa itama amma har lokacin wayar switch up. Tun tana danne damuwarta harta bayyana fili. Abbah da tun ɗazun yake kula da yanayinta ya tambayeta ko lafiya?. Batai nauyin bakiba tai masa bayanin abinda ya faru.      Shi dariyama ta bashi ganin yanda duk tai wani iri kamar ance Abdallahn ya rasu ne, dan haka yaɗan murmusa yana girgiza kansa, batare da ya ce mata komaiba ya cigaba dacin tuwonsa.         “Abban Abdallah dan ALLAH ko zaka kira min shi da wayarka?”. Sake kallonta yayi da ƙyau, sai kuma yay gyaran murya da ɗauke idonsa. “Khadija ki rage ruɗiyarnan taki, yanzu dan ALLAH Abdallah ƙaramin yarone halan? Maybe baida caji ne kokuma ya shiga wata sabgar. Kiyi haƙuri kiga zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu idan bai kiraki ba”.        A sanyaye tace masa “to” kawai badan hakan ya mata daɗiba. Sai ma ta tattare kwanikan daya kammala cin abincin ta fice da su. Saida takai kitchen sannan ta nufi ɗakin su Amal. Zaune ta iskesu suna karatu, Amal na ƙarama su Imran. Duk shiru sukai suna kallonta. Itama kallon nasu takeyi.       “Amal wanene a cikinku ya ɗaga kiran yayanku ɗazun?”.       “Kira kuma Momy? Wlhy bansan Yayah ya kira wayabama ni, dan tun ɗazun danace miki zanje na sake duba Nu'aymah ina can wajenta ɓangaren Hajjo ni da Yusrah. Amma wani abune ya faru?”. Kai momy ta girgiza mata tana kallon su Imran suma. Da ɗai-ɗai suka shiga bata amsar suma duk basu baneba.      Kanta taɗan dafe zuciyarta na neman faɗawa a ruɗani, lallai yaran sunada gaskiya, dan idanma tai dubi da lokacin da Abdallah ya kira ai duk basa gidan ma suna islamiyya. Kasancewar yau lahadi sunayin harta safe zuwa uku a tashesu, to indai suna garin suma yaran suna zuwa anan ma. Kuma tunda safen duk suka fita. Amal ce kawai batajeba saboda ta tashi da ciwon mara, daya ɗaga matane tace zataje ta duba Nu'aymah. Sai da ta fita da kusan awa ɗaya ma Abdallah ya kira.       Ficewa tai taja musu ƙofar tanason tunano ko wani ya shigo a wannan lokacin, to amma kuma babu wanda ya shigo ɗin, daga ita sai ƴan aikinta. Abba ma baya nan, Omar ma ganin datai masa bayan kiranne ya shigo gidan, dan tare suka fita da baba malam tunda safe.               Momy da taga tunaninta na kaita wasu nazari daban sai kawai ta ajiyesa gefe, ta barsa akan uzirine yayma Abdallah yawa. Waya kuma ƙila sanda yake kira cikin sauran ƙannensa yaran gidan wani ya shigo ya gani ya ɗaga.      Washe gari da safe batabi takan kiran Abdallah ba ta cigaba da hidimominta kamar yanda ta saba. Abin mamaki kuma har dare bai kirantanba, sai itace dai da dauriyanta ya gaza ta nemesa kusan taƙwas na dare. Switch up dai ɗin yauma.             Ganin yanda ta zuba tagumi yasa Abba jin tausayinta. Wayarsa yasa ya kira Abdallahn, amma sai yaji layin a rufe. maida kiran yay a ɗayar Number Abdallah ta business. Bugu biyu kuwa ya ɗaga. Bayan sun gaisa yace masa ga Momy.        Jimmm Abdallah yay kamar bazaice komaiba, sai da Abbah yace, “Nace ga Momynku ko bakajiba?”.          “Amm sorry Abbah network ne, bata to”.       Miƙama Momy Abbah yayi, ta amsa zuciyarta na mata sanyi, dan tana matuƙar ƙaunar Abdallah sosai a cikin ƴaƴanta, sai dai tana ƙoƙarin dannewa gudun saka ruɗani a tsakanin ƴaƴanta. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka karanta idan baka biyaba, karka kuma yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 _______________________             Da ƙyar Abdallah ya danne zuciyarsa ya gaida Momy da fuskarta ke shimfiɗe da murmushin farin cikin jinsa. Ta amsa masa cike da kulawa tana tambayarsa yaya suke? Ina Adawiya?.            Muryarsa a ɗan cinkushe yace tayi barci, shima shirin kwanciya yakeyi.            “To Alhmdllh tunda dai lafiya kuke. amma jiya miya samu wayarkane? Na kira har sau biyar baka ɗaga ba, daga baya kuma saima naji switch up”.            Ba ƙaramin haushine ya kama Abdallah ba dajin maganar Momy, bayan sharaɗin data gindaya masa mai ƙarfi akan abinda yake tsananin so shine kuma zata kirasa?, yanzu kuma dan taga tana kusa da Abbah take nuna kamar batai komaiba. To mizata faɗa masa bayan wanda ta faɗa masan kuma?............        “Abdallah lafiya kuwa?”. Momy ta katse masa tunani. “Babu komai Momy, wayarce ta faɗi a cikin ruwa bayan mungama waya jiya shiyyasa”.          “Abdallah ai ni bamuyi way.......” Zare wayar Abba yay daga kunnen Momy yana faɗin, “Haba Khadijah tunda kinji lafiyar tasu ya isa haka. Bakiga dare yayiba ne? Yanzu kuma Abdallah yanada iyali”.           “Afuwan Abban Abdallah na shafa'ane wlhy. Ni saima naji muryarsa kamar wanda bayajin daɗi”.       Kallonta Abba yay sosai, sai kuma ya matsota jikinsa ya gwargwaɗa mata magana a kunnenta. Idanu ta ɗan zaro waje, sai kuma tai saurin miƙewa tana kare fuska da hannu alamar maganar tasa ta bata kunya.      Murmushi Abba yay yana binta da kallo harta shige toilet. Yaɗan girgiza kansa yana gyara kwanciyarsa. ________________           Jikin Nu'aymah yayi sauƙi sosai Alhmdllh, sai dai har yanzu bata koma sashensu ba tana sashen hajjo. Tana dai zuwa ta gaishesu da safe, ta kuma taya Umm aiki kamar yanda aka horesu. Babu wanda yay mata maganar Yah Ab a gidan, itama tayi ƙoƙari ta danne tana jira taji daga garesu kamar yanda Yusrah ta bata shawara data dameta da tambayar yanda akayi.        Kwana biyu da samun lafiyar Nu'aymah su Momy sukai shirin komawa Abuja saboda karatun yara. A wannan karon Nu'aymah jitai batason tafiyar su Yusrah da Amal, dan suna ɗauke mata kewar Adawiya sosai. Tasan kuma idan suka wuce zata koma ita kaɗaine babu wani abokin ƙiriniyarta kamarsu a gidan, daga yayu sai ƙanne sai iyaye.         Babu yanda ta iya, a washe gari su Amal suka fara wucewa Lagos da safe. Da yamma kuma su Yusrah. Nu'aymah harda hawaye. Hajjo da taji tausayinta har tayi tunanin ko Nu'aymah tabi cikinsu Yusrahn, sai kuma ta tuna ashe akwai shirin zuwa ganin Doctor da sukeyi. Zama tayi taita lallashinta harta saki jikinta, yayinda su Hajarah da sukazo sashen Hajjon suka ɗan rage mata kewar tafiyarsu Amal ɗin. ★★★★★★            Kwanaki sun shuɗa, jikin Nu'aymah yayi garas, gidan ya koma kamar da sai su kaɗai. itama harma ta tattara ta koma ɗakinsu ita da Adawiya dake a sashensu. Sosai takejin kewar Adawiya, musamman ma idan tazo kwanciya ko zata shiga toilet. Dan ƙa'idane kullum sai sunyi faɗa akan bargo da filos, hakama shiga wanka sai sunyi faɗa. Haka sabo yake turken wawane.        A yanzun kam sai Muhammad ƙaninta ya zame mata abokin hira. Daya dawo makaranta koda yaushe suna tare, duk da dai ta dage wajen maida hankali a karatunta na islamiyya itama. Dan a ɗan tsakanin nan ba ƙaramin ƙoƙari takeyi akan haddar Qur'aninta ba. Ga sauran littatafai ta dage sosai suma.       Wannan karatun shine ya ɗauketa busy matuƙa. Tunma rashin sakewar da su Umm suke mata yanzu yana damunta har abin ya fara raguwar mata a rai. Dan tasha tambayar Umm ɗin kota musu wani laifine?. amma sai Umm ta shashantar da zancen taƙi bata amsa, haka shima Baba malam baya cemata komai akan hakan. A yaran gidan ma duk wanda taima tambayar ina Adawiya taje? Sai suce mata makaranta, Yah Ab kuma ya koma Saudia.       Takanyi shiru taita tunanin miyasa  za'akai Adawiya makaranta ita kaɗai a barta? Bayan kuma tunda suka taso komai tare sukeyi, makaranta da komai da komai tare ake sakasu, kuma tare ake musu komai. Wannan tafiya makaranta da taji na Adawiya saida ya sakata kuka, daga ƙarshe ta haƙura da fatan ALLAH yasa haka shine mafi alkairi. Tana kewar Yah Ab sosai a zahiri da baɗini. Gashi yanzu bata da waya, ta kuma kasa aron ta wani ta kirashi koda ta Umm ce. Dan da idan tanason suyi magana wayarta babu caji data Umm take amfani. Shima daya kira yaji bai sametaba zai kira Hajjo ko Umm a bata. Amma a wannan karon ganin shima ko sau ɗaya bai nemeta ba sai al'amatin ke ɗaure kanta da bata mamaki. Da taga dai zuciyarta na neman ƙuntata sosai sai taje ta tsare Hajjo da tambaya tana kuka.        Hankalin Hajjo ya tashi sosai. Ta zauna tana lallashinta amma Nu'aymah sai taƙi saurarenta. Tana cikin darzar kukan Baba malam ya shigo sashen hajjon da daddare bayan ya taso daga wajen karatu a massallaci.          Tsawa yayma Nu'aymah amma ba wadda zata sakata firgitaba. Tai saurin nutsuwa hawaye na sake rige-rigen sakko mata a kumatu.        “K wai kin koma jaririyane a gidan nan yanzu? Da zaki zauna kitama mutane kukan banza da wofi. Ki fita idanuna Nu'aymah tunkan na saɓa miki. Bake kika zaɓama kanki hakanba da kanki? To daga yau na baki sati biyu kima shi wanda kika gudu dominsa magana ya turo iyayensa”.          Cikin tashin hankali Nu'aymah ke kallon Baba malam. Bakinta na rawa tace, “Abbah wlhy ban guduba, dan ALLAH ka saurareni na faɗa maka yanda akayi”. “Bana buƙatar jin komai daga gareki Nu'aymah, dan saƙwannin da kika bar mana sun isheni dukkan amsa. To kin samu yanda kikeso. Kinso tozartamu ALLAH kuma ya hana faruwar hakan ya rufa mana asiri. Abdallah ne dai kince baƙyaso, ALLAH kuma ya canja masa da waɗanda suka fiki alkairi, sai kima wanda kikeson magana ya fito a aura masa ke kuje ku ƙarata”.       “A....Ab....Abbah!” ta kira sunan Baba malam bakinta na rawa da jikinta. Sosai kalamansa suka nema zautata. ‘Yah Ab ɗinta ne yay aure da wata ba itaba?. Kai ina bazai yuwuba ma’. Tai maganar a fili tana kallon Hajjo dan baba malam tuni yay ficewarsa ma.       Kamota Hajjo tayi ta rungume tana lallashinta. Tausayinta na ratsata. “Hajjo dan girman ALLAH kimin bayani, wlhy na kasa fahimtar kalaman Abbah gaba ɗaya. Da gaske yake Yah Ab yayi aure? Ya auri wata ba ni Nu'aymah ba?. Hajjo faɗamin dan ALLAH, taimakeni ki faɗain dan girman ALLAH hajjo”.           “Ya isa haka Zainabu. Ki nutsu na miki bayanin komai to kinji”.      Da sauri Nu'aymah ta shiga ɗaga mata kai tana share hawayenta da hannaye biyu. Hajjo ta ruƙo hanun nata, cikin nutsuwa tai mata bayanin komai daya faru a ranar bayan an wayi gari babu ita a gidan. Saƙwannin data ajiye musu akan ita ta tafi batason Abdallah sai Ameer. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka karanta idan baka biyaba, karka kuma yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 _______________________                  “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Mike shirin faruwa dani ni Nu'aymah? Hajjo wlhy kinji na rantse miki bani nabar saƙon nanba. Kuma Ameer da ake magana akansa ni babu abinda ya taɓa haɗani da shi sai sako da Yah Abdallah ke bashi yana kawomin. Rabon kuma dana sake ganinsa wlhy anfi wata huɗu Hajjo”.         “Ah ah! To amma shi kuma Abdullahin yace bai san Ameer ɗinba, bai kuma taɓa aiko wani wajenki ba sai Ahmadu”. “Bai taɓa ba Hajjo? Shi Yah Ab ɗin da kansa yace haka kuma?”. “Sosaima kuwa, a gaban kowama ya faɗa a randa al'amarin ya faru. Amma kwantar da hankalinki, Zainabu nima dai al'amarin nan ya ɗaure min kai matuƙa, yanda nasan kike da Abdullahi tayaya zaki aikata wannan abun? To amma iyayenki duk sun kasa fahimtar akwai wani ɓoyayyen al'amari daya faru a wannan ranar, musamman ma ɗan malam daya ɗauki zafi sosai akan al'amarin”.          “Hajjo dan ALLAH ki taimakeni, wlhy inason Yah Abdallah fiye da yanda kowa yake tunani, dan ALLAH ku tausaya mani karna rasashi hajjo. Idan na rasashi mutuwa zanyi......”         “Bazaki mutuba Zainabu kinji, ki kwantar da hankalinki muyita addu'a ALLAH na nan, yana sane da komai kuma shine maiyin maganin komai”.        Kai Nu'aymah ta ɗagama Hajjo dake share mata hawaye, ta kwantar da kanta a jikinta saboda kanta dake wani irin bala'in sara mata kamar zai tsage. “Hajjo kaina”. Hankalin hajjo ne ya sake tashi, dan sam ba'ason ciwon kai ga Nu'aymahr, daboda ciwonta. Saurin tada ita tayi daga jikinta ta kwantar da a kujerar tana faɗin, “Ina zuwa, bara na amso miki maganinki kisha”.         Hajjo da kanta ta nufi sashen su Nu'aymah dan yaran duk basu shigoba daga ita sai Nu'aymah ne kawai. Baba malam da Umm suna zaune a falo ta shigo, Muhammad na gefe yana homework.         Da sauri suka shiga tambayarta ko akwai abinda take buƙata?. Fuskarta babu ko ɗigon walwala tace su bata maganin Nu'aymah kanta ke ciwo. Ba ƙaramin faɗuwa gaban Umm yayi ba, amma saita danne ta tashi taje ɗakin Nu'aymahn ta ɗakko ɗan box ɗin da magungunanta ke a ciki ta kawoma Hajjo. Tanason taje taga mike faruwa da ɗiyar tata amma tanajin nauyin hakan. Ga baba malam yay kamar abin bai damesabama, ya cigaba da shan fruit salad ɗinsa hankali a kwance.      Hajjo dai batabi takansuba ta amsa tai ficewarta. Da kanta ta bama Nu'aymah maganin, sannan ta kamata ta kaita bedroom ɗinta ta kwantar. Cikin amincin ALLAH babu jimawa barci yay gaba da ita.           Washe gari da zazzaɓi Nu'aymah ta tashi ga ciwon kai. abinda ya tada musu hankali Doctor ɗinta yayi tafiyar da yace, gashi kuma basu nema wancan likitanba. Andai kaita asibiti wani likitan daban ya dubata, yaɗan mata abinda zai iya ya turasu asibitin dawanau. Kamar koda yaushe Baba malam yaƙi yarda a kai Nu'aymah dawanau, dan acewarsa yarinyarsa ba ciwon hauka take ba. Yasan dai ance tanada matsala a ƙwaƙwalwa. Hakan yasa ya ɗakko file ɗin Nu'aymah da shirin neman wancan Doctor ɗin. Amma abin mamaki da al'ajabi babu takardar da Numbers ɗin take. Anyi ɗai-ɗai da file ɗin babu ko alamar takardar. Kamar wasa aka bincike littatafan baba malam dake tare da file ɗin tas babu takardar dai.      Wannan al'amari ba ƙaramin ɗaure kan kowa yayiba a gidan. Musamman da ya zam agaban kowa Doctor ya bada takardar da file ɗin. Wannan al'amari ya sake ɓata ran baba malam matuƙa, amma jarumar fuskarsa taƙi nuna hakan. Sai Hajjo ce keta masifa kamar zata haɗiye harshenta. Dan wannan ɗauke takardar ya sake tabbatar mata da akwai mai yin ƙulle-ƙulle a gidan da gaske. Sai dai yanda kowa ya nuna damuwarsa akan al'amarin baka isa nuna zarginka kai tsaye akan wane ne ɗin ba. _____★_____                “Maganar gaskiya al'amarin gidannan ya fara bani tsoro Abban Nu'aymah. Anfa daɗe ana ruwa ƙasa na shanyewa, dolene a wannan karon nasan wanene ke mana SARAN ƁOYE. Tunda har aka iya toshe hanyar neman lafiyar Nu'aymah lallai za'a iya kashe mana ita ma”. Umm tai maganar hawaye na zuba mata masu zafi.           Zama baba malam daketa kai kawo a ɗakin yay kusa da Umm, ya kafeta da idanunsa da sukai jajur shima saboda damuwa. “Jannat idan munce zamu ɗauki mataki, akanwa zamu ɗauka? Akan kuma mi?”.        “Amma Abbah Nu'aymah karka manta musabbabin ciwon Nu'aymah fa faɗo da ita akai daga kan gado tun tana jaririya, kanta ya bugu ta samu ciwo a ƙwaƙwalwa. Badan ALLAH ya taƙaita wahalaba da zata tashine cikin halin rashin hankali kamar yanda Doctor ya sanar mana. Addu'a da hikimar UBANGIJI ce ta cigaba da jagorancin lafiyar Nu'aymah hartakai wannan lokacin cikin hankalinta, sai dai idan ciwon ya motsa tasha wahala. Tun Nu'aymah batasan ma'anar magani ba ake ɗura matashi a ciki, kanaji kwanaki badan ALLAH yasa Doctor ya farga ba hantarta fa harta harbu da ciwo saboda yawan shan magani. Abban Nu'aymah baka tunanin game da al'amarin aurenan akwai wani abu da bamu hasasoba kuwa?”.            “Kiyi haƙuri Jannat karmu zargi kowa akan al'amuranmu, mu daure mucigaba da ɗaukar komai akan jarabawa ne. Duk abinda yay farko nasan zaiyi ƙarshe. Da ALLAH na dogara game da lafiyar Nu'aymah nasan kuma shi mai jine mai kuma ganine. Indai bamu da haƙƙin kowa ALLAH bazai bama kowa damar shiga haƙƙinmu ba. Ki kwantar da hankalinki, insha ALLAHU zan sake samo Number likitan nata, dan mantawama nai nace masa idan ya tafi ya kiramu”.            Kanta ta jinjina masa hawaye na cigaba da sauka mata. Ya saka hannu ya share mata yana murmushin da shima iyakarsa laɓɓansa ne kawai. Shi kaɗai yasan mi yakeji a ransa. Yana dai ƙoƙarin dannewane dan yasamu Umm ta kwantar da nata hankalin kodan hawan jininta............✍ _____________________ SAHFAT PREORDER! ______________________         Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗. SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya. Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske. *_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._* _To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_. Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU. Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa. *_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_* _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* No. 10 ________________________ *ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*        *_KAJI shahararrun kuma mandiyoyin ƴan ƙwalisar kawo kayan kitchen masu tafiya dai-dai da zamani. Idan nace nadaban ina nufin suɗin nadabanne wajen kaya ƴan gaske dake ƙawata kitchen ɗin amarya harma dana uwargida ƴar ƙwalisa. Ka siya ka tabbatar ka saya ɗin ko a gaban tsaranka sai *ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*. sunan kayansu sa kishiya cin bashi🤣, dan tana ƙyalla ido taga kitchen ɗinki tsarin amerikawa tuni zata fara ƙwafa da tunanin zuwa gidan delu dillaliliya mai saida kwanika. Sai dai kuma kama da wane akace bata wane, dan haka ku maza ku garzaya ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*  domin samun naku kuma. Suna kawo kaya daga ƙasashen ƙetare akan farashi mai sauƙi da rahusa. Suna order ɗin products kamarsu, dukan kayan kitchen na zamani, bedsheets, shoes dade sauransu, products ɗinsu pre-order ne dake zuwa akan lokaci batare da mai kaya ya ƙosa da jira ba ko samun matsala. Zaku iya samunsu a Number waya kamar haka ko Location nasu. Phone number: 08102393622. Location Gombe. Amma Zasu iya turawa kowani gari dake a lungu da saƙo na ƙasarnan. Sayen nagari maida kuɗi gida. Ku garzaya kar ayi babu ku. Da ƙyar nasha yafi da ƙyar aka kamani inji masu iya magana😉😘😘😍😋._*      _________________________ .............Yau Nu'aymah ta tashi jikin nata daɗan dama, sai dai rashin ƙarfin jiki. Tunda Ahmad ya tafi raka Hajjo asibiti ganin Doctor saboda ƙafarta saita dawo sashensu ta kwanta. Barci tai sosai dan har sai gab da azhar ta tashi tai wanka. Shiri tai da ɗan sauri-saurinta ta fice zuwa ɗakin Umm, dan wani irin maitan awara takeji. Babu kowa a ɗakin, sai gyara da yasha yanata uban ƙamshi. Tai murmushi da faɗawa saman gadon ta kwanta tana mai sake shaƙar turaren wutar da ƙyau cikin hancinta. Tana masifar son ƙamshi a rayuwarta. Shiyyasa turare kwana kaɗan yake mata ya ƙare. Ga baba malam da Yah Ab sun mugun ɗaure mata ƙugu wajen siya mata. Sam basa gajiyawa. Kafin wani ya ƙare an saya mata wani. Ga khumra da Umm itama take bata ita da Adawiya. Tun Adawiya bata damu da ƙamshiba harta fara biyema Nu'aymah saboda yanda take bulala musu shi a cikin ɗaki kamar shagon saida shi.........           “K! Kuma yaushe kika shigo nan?”. Umm ta faɗa tana kallon Nu'aymah dake kwance a kan gadonta idanu a lumshe.      A hankali ta buɗesu akan Umm dake kallon yanda tai rama cikin kwanaki kaɗan. Tai ɗan ɓata fuska kamar zatai kuka. “Umm dan ALLAH awara zanci”. Kai Umm taɗan girgiza da nufar gaban mirror ɗinta ta ɗauki ƙaramar wayarta da tazo ɗauka. “Indai banda fitina ni ina naga awara yanzu Nu'aymah? Ke dai inhar kikai zazzaɓi sangarta iri-iri kin iyata mara dalili, ko Muhammad baya iya shegenki a gidan nan”.               “Umm Please!”. Ta sake faɗa cike da shagwaɓa kamar zatai kuka. Zama Umm tai a bakin gadon kusa da kanta. Taɗan shafa goshinta a hankali,  “Nu'aymah banson rigimar nan, yanzu dai kinsan baza'a samu awaraba ko? Sai ki bari sai anjima, bara dai na bama Saude takai kuɗin gidan ƴan awaran”.       Kai Nu'aymah ta ɗagama Umm tana murmushi, sai kuma ta tashi zaune ta rungumeta tana ƴar dariya. Zame hular kanta Umm tai ƙoƙarin yi. Da sauri Nu'aymah takai hannu zata riƙe dan tasan mi Umm ɗin zata duba. “Umm kainafa ke ciw.....”         “Ƙaniyarki keda ciwon kan, wai Nu'aymah bazaki daina wannan shegen ƙazantan nakiba na rashin son ƙitso? Kalla kiga fa kanki gashinki duk ya lalace saboda rashin kula. Tashi maza ki wuce wajen Adda ta kama miki kai kafin na ɓata miki rai”.          Ƙwalla cike da idonta ta kalli Umm, “Umm dan ALLAH ba yau ba”. “Kin rainani ko?”. Umm ta faɗa tana ɓata fuska.       Muhammad dake ƙoƙarin shigowa ya ƙyalƙyale da dariya yana faɗon, “Umm ALLAH fa ta rainaki, inba rainiba ya zakice taje kitso ta zauna shagwaɓa......”     Filo Nu'aymah ta ɗauka ta wurgama Muhammad ɗin. Ya goce yana dariya. “Wlhy idan na kamaka a gidannan saina tsiyayar maka da man kai tas. Umm ki faɗama yaron nan nifa ba sa'arsa bace”. Yanda tai maganar idanunta cike da ƙwala ya saka Umm yin ƙaramar dariya itama, tai saurin saka hannu ta rufe bakinta tana haɗiyeta ganin hawayen harsun sakko a guje.       “Uhghumm!” Umm tai gyaran murya tana haɗe fuska da wurgama Muhammad harara. Hannayensa ya haɗe waje guda fuskarsa da murmushi yace, “Am Sorry aunty N”. Ya ƙare maganar da mata gwalo kaɗan. Harara ta zuba masa ta koma ta kwanta da juya masu baya shi da Umm ɗin.        Hannu Umm ta bashi suka tafa, kafin ya haye gadon yana faɗin, “Banace kiyi haƙuri ba Noorunnisa”. Juyowa tai fuskarta ɗauke da murmushi ta dungure masa kai tare da ja masa hanci tana faɗin, “Yaro 1-0”.       Dariya sukayi a tare. Umm ta miƙe tana murmushi ta bar musu ɗakin. ★★★★        Sashen Addah Umm ta nufa, dan tanason su tattauna game da al'amarin nan na Nu'aymah tun jiya, sai dai rashin lokaci yasa bata shigaba. Tasan itama Addahn bata shigo bane saboda taga baba malam ya wuni a gida jiya, yauma ya daɗe bai fitaba.               Kubrah kawai ta iske a falon tana  yankan ƙumba. Ta gaidata cike da girmamawa kamar yanda suka saba. Dan bayan mahaifiyarsu Umm itace mace ta biyu a gidan da suke ɗauka tamkar mahaifiya. Fuskar Umm ɗauke da murmushin itama ta amsa mata, “Ɗiyata saike kaɗai a gidan kenan?”. “Eh Wlhy Umm, daga ni sai Addah kawai. Hajarah da su Jafar sun fita aika”. “To ALLAH ya maidosu lafiya. Ina Addan?”. “Umm tana ɗaki ki shiga mana”.      Kafinma Umm ta amsa mata Addah ta fito daga ɗaki. “Haba nifa ince kamar muryar Umm, ashe kuwa kece?”. “Ƙyaface haka mana, tun jiya rabon danaga idonki a gidannan Addah. saboda kinga ƴarki ta samu lafiya”.                “Wacefa lafiya Umm, anason a ganmin bayanta”. Addah ta faɗa cikin ɓacin rai. Murmushi Umm tayi da kama hannunta, dan tasan Addah dama bata barin saita kwana sam. “Kinga nidai muje sarkin hawa”.            “Bazaki ganeba Umm. Daga jiya zuwa yau naje sashenki yafi sau a ƙirga amma sai na iske Baba malam na nan. Wlhy na kwana tamkar na ciji kaina dan baƙin ciki. Gaskiya Umm wannan al'amarin bai kamata mu zuba masa idanuba a wannan karon, yanzu dan ALLAH minene na ɗaukar Number wayar likita idanba zalunci ba? Lafiyarta ne ba'ason anema kenan ko minene?”.           “Humm Addah wlhy nama kaina wannan tambayar yafi sau dubu tsakanin jiya zuwa yau. A a daren jiya har musabbabin ciwon Nu'aymah sai da ya dawomin a rai. Bansan minene laifin yarinyar nanba akeson rayuwarta ta salwanta. Ni harma na rasa wane kalar tunani zanyi Addah, wanene? Miyasa? Mi mukai masa?......”             “Umm nidai tsakanina da ALLAH na fara zargin jama'ar gidan nan fa, idan har mai aikata wannan abubuwan ba'a gidan nan yakeba to daga ina yake zuwa? Nifa dagama jiya na fara tantama akan barin Nu'aymah gidan nan akan maganar aurenta. Shiyyasa ni dama tun farko ban yardaba. ni dama tun jiyan wani shawarace tazomin akan yanda zamu saka ido akan motsin kowa, na tabbatar insha ALLAH a hankali zamu samo bakin zaren”.                 Kai Umm ta ɗaga mata cikin alamar nuna gamsuwa. Addah ta matso kusa da kunnen Umm ta gwargwaɗa mata hanyar daya kamata subi. Ɗari bisa ɗari Umm ta amince, suka ɗaura da addu'ar dacewa. Daga nan suka cigaba da tattauna al'amarin suna ƙarama juna haske. Umm bata bar sashenba sai da lokacin salla yayi. Ta koma sashenta tana jin daɗi a ranta, koba komai zuciyarta ta rage nauyin da tai mata. Shiyyasa akoda yaushe take sake godema ALLAH daya haɗasu aure gida ɗaya ita da aminiyarta. Su kashe su rufe matsalolinsu babu maiji sai ALLAH.             ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka karanta idan baka biyaba, karka kuma yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 _______________________ _____________ *_DUBAI_* ________                  Tun randa Abdallah yay waya da wadda yake zaton Momynsa ce ransa ya sake dagulewa gaba ɗaya. Wani lokacin ji yake tamkar ya naɗama Adawiya mugun duka ya cillata jirgi ta koma Najeriya. Sai dai tsoron fushin iyayensa ke sakasa dannewa.          A maimakon kwanaki bakwai ɗinma da yay niyyar suyi a kwana na huɗu yasa suka wuce Saudia. Adawiya sai jin daɗi takeyi dukda bata ganin koda murmushinsa. Ita kasancewa da shi a ƙarƙashin inuwa ɗaya kawai ya wadatar da ita a cewarta.        Ba wannan bane karonta na farko zuwa ƙasar saudia, sai dai yanda tazo a wannan karan yanada banbanci da sauran zuwanta na baya. Shiyyasa take wani jin kanta a sama. Wanda kuma takeyi dominsan ma baisan tanayiba. Tunda suka iso gidan da zasu zauna ya nuna mata ɗakinta bata sake ganin koda ƙeyarsa ba. Tsalle ta dingayi bayan fitarsa, dan ɗakin yayi matuƙar ƙyau da tsari. Sai dai kalar komar zaɓin Nu'aymah ne, harda ma manyan frames ɗinta guda uku da aka manna a bango, sai na Abdallah guda biyu shima. Dukansu sunyi masifar ƙyau. Ta taɓe baki da jan wawan tsaki, stool ɗin mirror taja duk ta juya na Nu'aymah dan har cikin ranta ta tsani ganinta, tunda itace sanadin hana tabbatar farin cikinta, saboda Nu'aymah yah Abdallah yaƙi sake mata, saboda Nu'aymah ta gagara daraja a garesa matsayinta na matarsa. Saboda Nu'aymah saboda Nu'aymah..... Komanta yaƙi dai-daita kamar yanda tai fata, tabar na Abdallah kawai tana faman kuka kashirɓan da zagin Nu'aymah da batasanma tanayiba.            Rayuwarsu ta saudia tana kadaran kadahan ne, baya shiga harkarta bakuma ya takura ma rayuwarta. Sai dai har yanzu ya hanata wayarta, idanma zata gaisa da Addah da Abbanta ko wani a ƴan gidan nasu saita wayarsa. Kuma yay tsaye a kanta har saita gama ya amshe abarsa. Hakanna bata haushi, amma sonsa da tsoronsa ya hanata ta nuna masa koda a fuska.       A haka suka kwashe watanni biyu a gidan. Shirye-shiyen makarantarta ya gama kammaluwa ta fara zuwa. Da farko bata shiga harkar kowa ta maida hankalinta a karatu kamar gaske. Tana wata na biyu da fara karatunta tai ƙawa mai suna Abida, sai da ana kiranta Maman Aaida, itama matar aurece harda yaranta biyu, asalin Mamana Aaida itama ƴar Nageriya ce, amma yanzu iyayenta na nan Saudia. Ta girma Adawiya da kusan shekara uku zuwa biyar, dan itakam zatai 22years. Maman Aaida irin matan nanne masu shegen iyayi dason gayu, ga Ƙwanƙwanin tsiya kamar jikar ƙaruna, kullum cikin bama Adawiya labarin mijinta take a zatonta Adawiya budurwa ce. Adawiya dataga iyayin Maman Aaida yayi yawa saita fito ta nuna mata itama ai tanada auren. Sosai Maman Aaida tayi mamakin hakan, danta tabbatar saita shirya zuwa gidan Adawiya a wani weekend. Babu wani ja'inja Adawiya ta bata address ɗinta. A kuwa ranar Alhamis saiga Maman Aaida har gida ita da maigidanta da yaransu biyu, da yake Abdallah na gida sai har mijinma ya shiga. Abdallah dai bai wani sake musu ba, bai kuma wulaƙantasuba aka gaisa da ƴar hira suka wuce, bayan tafiyar tasu kuma bai cema Adawiya komaiba akan zuwan nasu ba duk da yasan ya dace ace yayi hakan.            Sanadin haɗuwa da Maman Aaida fa idanun Adawiya ya ƙara buɗewa. Dan tunda Maman Aaida ta bigi cikinta taji yanda akai aurenta da Abdallah sai ta shiga ɗorata bisa wasu hanyoyi da zata ringa jan hankalin Abdallah, ciki harda abubuwan irinsu turaren jan hankali da sauransu. Tun Adawiya najin tsoron yin hakan harta fara hawa kan network da sha'awar fara gwadawa ko zata dace Abdallah ya manta da Nu'aymah.       A ranar farko da ta fara buɗe jikinta da turare Abdallah bai kwana gidanba, yamayi tafiya bata saniba. Da yake sai ya gadama take ganinsa sai bata fahimci baya nanba, washe gari ta wuce makaranta. Data dawoma bata gansaba bata kawo komai a ranta ba har dare, lokacin kwanciya ta sake shanana turare ta nufi ɗakinsa. Sai dai kuma wayam. saida ta leƙa har toilet sannan ta lurama ba'ai amfani da toilet ɗinba ma kwata-kwata. A take kuma sai tsoro ya kamata duk ta tsure, leƙe-leƙe ta shigayi cikin gidan kamar wata zararriya. Data ga dai lallai babushi a gidan saita fara kuka, ta koma ɗakinsa ta ƙulle ƙofa ta ƙudundune a bargo. Ta kusa awa guda a haka sannan ta fara jin motsin za'a buɗe ƙofa. Sake rikicewa tayi da kuka catake wanine ya shigi. Cike da mamaki Abdallah daya shigo yake sauraren kukan nata dan baiyi zaton ganinta a ɗakin nasa ba. Ƙarasawa yay gaban gadon ya yaye bargon. Tako dage zata kwarara masa ihu dan ruɗewa ya hanata nutsuwa taga wanene. Saurin hayewa gadon yayi ya rufe mata baki ruf da hannunsa yana kallon yanda jikinta ke rawa.         A take yanayin nata ya juye masa tamkar na Nu'aymah, dan duk lokacin da abu ya tsoratata haka zakaga jikinta na rawa duk ta fita hayyacinta, daga haka kuma saita suma. Yanda zuciyarsa ke ƙawata masa Nu'aymah sai tunaninsa ya gushe zuwa gareta harya rungume Adawiya batare daya fargaba. “K malama ki nutsu nine?”.          Sosai Adawiya ta sake maƙanƙale masa dan a rikice take sosai, amma taji daɗi da taji shine.             Tun Abdallah na shaƙar ƙamshin turaren data saka matsayin ƙamshi kawai harya fara canja masa yanayi. Hancinsa ya ɗaura bisa wuyanta yana shinshina da lumshe idanu, kafin a ɗauki tsahon lokaci jikinsa ya fara tsuma, sai ya sauya salon riƙon da yay mata. Anan nefa Adawiya ta dawo hankalinta da ƙyau. Da farko nishaɗin abinda yake matan ta farayi. Sai dafa taji al-amarin bawai wasan yara bane sannan ta fara kuka da roƙo da magiya. Da al-amari yay zurfi saiga hajiya malama mandiya ƴar ƙwalisar soyayya Adawiya na tsinema Maman  da jamata ALLAH ya isa🤣😂🤣.      Oho, Abdallah baisan tanayiba, morewarsa yakeyi dai-dai gwargwado, yama manta dawa yake tare. Iya wahala ya bama Adawiya batare da tausayawaba, kafin ya koma gefe ya barta ko numfashin kirki bata iya yi.       Tun daga wannan ranar Abdallah ya maida Adawiya abar hutawarsa. Daya samu biyan buƙatarsa kuma ya watsar da ita tamkar bai taɓa sanin daga inda ta fitoba. Sam ta gagara gane kansa balle inda ya dosa. Komai nasa yana yinsane da kulawa da lura. Abincinta dama kam bai taɓa ci ba, zai dai ajiye mata duk abinda ta buƙata ya kuma bata kuɗi. Amma babu wani farin ciki da kulawa kamar yanda Maman Aaida ke faɗa mata. Duk iya dabarun Maman Aaida cikin gwadasu take ga Abdallah amma saiya yi kamarma baisan tanayiba. ba shiga ɗakinta yakeba, ko abu zai bata sai dai yay knocking ta fito ta amsa. Idan yana buƙatar moranta ma zai mata knocking ne idan tana ɗaki yace ta samesa nasa ɗakin.      A haka rayuwar auren nasu ke tafiya tare da karatun Adawiya da ta fara saka shiririta saboda damuwarta kawai itace Abdallah ya sota a yanzu. *_NAJERIYA_*             Rayuwa ta shuɗa, kwanaki nata gangarawa, inda ake neman watanni na takwas kenan da lalacewar auren Nu'aymah da Abdallah. Tana cikin tsananin damuwa da begensa, kullum dare sai tayi kuka, tana sonsa matuƙa, dan ta rayune da son nasa. Yawan damuwar da take a cikine ya haifar mata da yawan yin ciwo, saboda ciwonta bayason damuwa sam. A duk sanda ta takura kanta da tunani da damuwa yakan yawaita motsa mata akai akai, tana kuma matuƙar shan wahala.         Gaba ɗaya a awatannin nan lafiya taƙi wadatarta, haka taketa fama yau fari gobe tsumma. Gashi baba malam kullum cikin mata jan ido yake akan ta kawo Ameer yay musu aure. Tayi kuka tayi rantsuwar akan Ameer ba saurayinta bane amma sam yaƙi ya saurareta. Umm kanta wannan al'amari na tada mata hankali. Amma babu yanda ta iya ta zuba musu ido kawai taga iya gudun ruwan mijin nata.           Burin Nu'aymah cigaba da karatu a yanzun, amma Baba malam yay banza da maganar karatun nata, bayan kuma kowa a gidan yasan burinta a rayuwa shine ta zama likita ko Nurse tun tana yarinya. Addu'arta kullum itace Baba malam ya haƙura a sake nema mata makaranta kafin ALLAH ya dawo da hankalin Abdallahnta gareta, dan ita duk ɗaukarta Abdallah fushi yake da ita akan ta gudu ran aurensu, shiyyasa yaƙi nemanta koda a wayama. Ta dage da azumin litinin da alhamis da sallar dare tanata gayama UBANGIJI kukanta.       Ana cikin wannan yanayin su Baba malam suka gama shirya gagarumar walima na saukar Al-Qur'anin yaransu na gidan marayu, tare da aurar da waɗanda suka samu mazan aure. Wasunsu anan cikin gidan suka dai-daita kansu. Wasu kuma a waje suka samu mazajen aure da mata.     Shirye-shirye ake babu kaman hannun yaro, dan shinema ya ɗauki Baba malam Busy sosai ya samawa Nu'aymah lafiya daga takurar zancen fiddo mijin aure. Duk da dama dai yana matane kawai dan hukuntata ta cikin ruwan sanyi akan abinda ya faru. amma ta ƙarƙashin ƙasa neman hanyar ganin likitan nan kawai yakeyi da nema mata makaranta batare da ko Umm ta san da hakan ba.        Ana saura sati ɗaya su Yusrah suka iso, washe gari kuma su Amal. Hakan ba ƙaramin daɗi yayma Nu'aymah ba, koba komai ta rage kaɗaicin da ta tsinci kanta a cikin a waɗannan watanin ai. Abinda ya ƙara faɗaɗa farin cikin natama shine Amal da Yusrah bazasu komaba, dan zasu zaunan zana jarabawar ssce anan. Cikin kwana biyu kacal da dawowar tasu ta fara komawa cikin walwalarta.        Tuni suka fara addabar gidan da ƙiriniyarsu da bata ƙarewa, sauƙinma babu Adawiya, amma hakan baisa sun fasa abinda suka saba yiba. tun ana saura kwana uku suka saka Hajjo ta roƙa musu baba malam komawa cikin gidan marayu har sai an kammala komai. Dan yawancin ƴammatan da za'aima auren duk ƙawayensu ne, duk da dai a shekaru gaskiya zasu girmesu da kusan shekara bibbiyu ko ɗai-ɗai.      Bai hanasu ba, dan gidan marayun nan nada matuƙar muhimmanci a garesa dama family ɗin gaba ɗaya. Yanda suke ƙoƙarin dagewa akan tarbiya da karatun yaransu haka suke dagema yaran gidan marayun nan suma. Shiyasa suma yaran suna tsananin ƙaunar wannan family, su suke ɗauka danginsu da komai a rayuwa. ★★★★★              “Wai wannan akwatin da kika lodama kaya duk na miye Nu'aymah?”. Umm data shigo ɗakin Nu'aymah ta faɗa tanabin Nu'aymahr daketa shirin kaya da kallo.      Ɗagowa tai ta kalli Umm cike da ɗoki, “Umm yo na bikine mana, sati guda zamuyi a can”.  “To lallai, ashema kune iyayen bikin kenan?”. Dariya Nu'aymah tayi dajin zancen Umm, Umm kam daga haka bata sake cewa komaiba ta ajiye mata magungunan ta tana faɗin, “Gasu nan, saura kije kita wasa da shansu Nu'aymah, dan ALLAH ki kula da kanki, duk abinda kikasan zai zame miki matsala ki kujesa, ku kuma riƙe mutuncin kanku, na kira Baba Habi a sashenta zaku zauna kafin Hajjo ta iso gobe idan ALLAH ya kaimu, saura naji wani abu mara ƙyau na shegen tsiwanki, ALLAH saina ɓata miki rai”.         “Umm insha ALLAH bazakiji komaiba ma”. “ALLAH yasa”. Umm ta faɗa tana juyawa ta fice daga ɗakin..           Bayan sallar azhar su Nu'aymah sukai sallama da kowa suka wuce, Yah Abubakar ne ya kaisu. Da yake shima irinsu ne ɗan taraliya saida ya kaisu sukai shopping sannan ya wuce dasu gidan marayun.      Ƙaton gaske ne, sannan an ƙawatashi ta ko ina babu makusa. Akwai makaranta da asibiti da duk ma abinda masu rayuwa da iyayensu suke samu. Makarantarsu ta fara tun daga noziri har zuwa sakandire. Ana koyar da boko da arabic, idan kaji yanda yaran ke larabci da turanci sai kasha mamaki da al'ajabi. Rayuwarsu suke cike da farin ciki da jin daɗi wadda ko wasu masu iyayenma basa samu. Gasu da tarbiyya abin birgewa.      Ɓata lokacine zama bayyana muku yanda gidan marayun nan ya ginu da tsari mai ƙyau, kusa a ranku kawai ya haɗu. Dan sosai su baba malam ke samu taimakon manyan mutane dama masu mulki game da riƙe gidan. Ga kuma suma kansu masu nemane basu zauna jiran na sadakaba. Kaso mafi yawa na ɗunbin dukiyarsu yana tafiyane wajen tattalin rayuwar marayun nan da kulawa da su. Shiyyasa Alhmdllh da wahala ace sun nema abu sun rasa. Sai dai ace yau da gobe sai ALLAH, komai arziƙinka dama wani abun sai ya gagareka.        A yanda su Nu'aymah suka sami tarba zai tabbatar maka da sanannune a gidan, kuma ba wannanne farkon zuwansu su kwanaba. Dan rigima aka shigayi musamman ga sa'anninsu, kowa na faɗin sashinsu su Nu'ayma zasu sauka. Bayan ansha taƙaddama dai kowa ya haƙura zasu zauna a sashen da amare suke, wato sashen baba habi da Umm ta faɗama Nu'aymah tun a gida.         A yau kowa ya kalli Nu'aymah yasan tana cikin farin ciki sosai, haƙoranta sun kasa rufuwa. Tsiyarsu sukaita tsulawa uwa ba kwaɓa uba babu tsanani, dan suna son suga sunzo gidan nan, shiyyasa wani lokacin baba malam da kansa yake cewa suzo suyi weekend ɗinsu anan, dama anan duk yaran gidansu ke karatunsu tun daga noziri har zuwa sakandire, shiyyasa sukeda shaƙuwa sosai da yaran gidan marayun fiye da zaton mai tunani.      Washe gari Nanah tace suma gasunan zuwa ita dasu Suhailat, hakan yasa bayan sallar la'asar ana tsaka da musu ƙunshi dan ranar itace suka saka ranar ƙunshin, Nanah ta kira wayar Yusrah ta sanar musu gasu a bakin titi suzo su shiga dasu dan baza'a barsu su shigaba kai tsaye.         Nu'aymah da Yusrah da biyu cikin ƴammatan gidan suka fita shigowa da su Nanah dansu ƙunshinsu harya bushe sun wanke, Nu'aymah ce kawai bata wanke nata ba amma ya bushe. da ƴar tafiya tsakanin gate da gidajen yaran, amma haka suka taka a ƙasa suna hira har suka iso. suna a gab da fitane suka haɗu da yaran gidan maza da bazasu gaza shekaru sha biyu ba kusan su bakwai wai wajen ball suka tilla ƙwallon waje ta katanga shine zasu zagaya ɗakkowa. Security ɗaya ne tare dasu zai rakasu. A tare suka fita dasu Nu'aymah da zasuje tarbar su Nanah.        Gidan marayun yana akan babban titine, shiyyasa sam ba'a barin yaran fitowa ko ina su kaɗai koda hakan ta kama sai da security.               Dariya Nu'aymah tai ganin su Nanah acan ɗayan tsallaken basu tsallakoba, tasan Nanah matsoraciyace akan tsallaka titi dama, shiyyasa yanzuma abun ya bata dariya data tuna. Su Yusrah ma dariya suka sanya famhimtar dariyar Nu'aymah da sukayi. Bayan sun kalla ɓangare biyu na titin babu mota suka sa kai zasu tsallaka. Da sauri security ɗin daya rako yaran nan yasa hannu ya fisgo Nu'aymah dake ƙarshen tafiya saboda tahowar wasu motoci guda uku a jere cikin masifaffen gudu.         Ta juya zataima security ɗin masifar taɓatan da yayi dukda tasan hakan na halinsu bane sukaji razananniyar ƙarar ɗaya daga cikin yaran wanda motar farko ta kwashesa yana ƙoƙarin ɗakko gyalen Nu'aymah daya zame ya faɗi lokacin da security ɗin nan ke ƙoƙarin maidota baya.          “Ƙuuuuuwww!!!” motocin suka bada sautin taka birki a tare, yayinda mai napep dake bayansu ya bugi motar ƙarshe shima.       A tare su Nu'aymah suka fasa ƙara da rumtse idanu kunnuwansu a toshe da hannayensu, sai da sukaji tsitt sannan suka bubbuɗe ido dan son ganin yaya akayi.        “Innalillahi.... Suka shiga ambata kusan a tare saboda hango yaron a kwance ƙasa cikin jini. Sunma manta a titi suke, suka tafi da gudu kansa suka rufu masa. Sunkai mintuna uku akan yaron nan suna kuka da jujjuyashi amma ko mutum ɗaya bai fito daga motocin nan uku ba balle kai tunanin sunsan ma abinda suka aikata. Cikin tsananin fushi da zafin zuciyar gado Nu'aymah ta rarumi wani dutse dake a gefen titin ta nufi motar tsakkiya dake a saitinta, wadda kuma tafi kowacce haɗuwa da ƙyau ta buga dutsen jikin glass ɗin.       Ko gezau glass ɗin baiyiba, dan haka ta koma na gaba wanda tasan insha ALLAH zata dace ta sake bugawa da iya ƙarfinta. Aiko a take ya shiga tsatstsagewa. Ta sake ɗagawa zata buga aka riƙe mata hannu. Fisge hannun nata tai ƙoƙarin yi ta kasa, dan haka ta juyo bakinta cike da tsiwa.       Ido huɗu tayi da manyan garada masu suffar ƴan dambe cikin baƙaƙen suit da glasess zagaye da ita su shidda, daka gansu kaga cikakkun marasa imani dan babu alamar sunsan ma minene dariya a rayuwarsu, babu tantama kuma zasu iya halaka mutum batare da sunji koda ɗar ba.         A mamakinsu sai gani sukai ta ɗaga dutsen ta bugama wanda ya riƙe mata hannu a goshi. Saurin sakinta yay ya dafe goshinsa daya fashe a take ya fara zubda jini.         Kusan a tare suka fiddo bindigu suka nunata da shi. Duk da Nu'aymah tasan zasu iya harbin nata ta mutu kuma, amma sam cikin idanunta babu tsoronsu, saima masifa dake cinta. Haka take ita sam batasan tsoroba. Idan kaga tsoro ga Nu'aymah to duhu ne ko tsawa, ko allura.        Ɗasss! Ɗasssss!! Ɗassssss!!! Sukaji sautin buga yatsu a bayansu. Gani tai duk sunja baya daga kusa da ita amma basu sauke bindugunba, sundai risinar da kawunansu ƙasa na alamar girmamawa ga koma wanene mai buga yatsun.         Kamar bazata juyaba sai zuciyarta ta bata shawarar juyawa taga wane shahararran ƙwallan mara imanine da mutuncine shiɗin...........✍ Nidai nama rufe idona bazan gansa ɗinba😎🚶🏻. Yau dai ga dogon page nan ku more harda na jiya na haɗa muku. Saura kuma naji wata tace bai isheta ba😚😏😣🚶🏻🚶🏻🚶🏻 __________________________________ _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_* No. 11 ________________________ *ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*        *_KAJI shahararrun kuma mandiyoyin ƴan ƙwalisar kawo kayan kitchen masu tafiya dai-dai da zamani. Idan nace nadaban ina nufin suɗin nadabanne wajen kaya ƴan gaske dake ƙawata kitchen ɗin amarya harma dana uwargida ƴar ƙwalisa. Ka siya ka tabbatar ka saya ɗin ko a gaban tsaranka sai ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE. sunan kayansu sa kishiya cin bashi🤣, dan tana ƙyalla ido taga kitchen ɗinki tsarin amerikawa tuni zata fara ƙwafa da tunanin zuwa gidan delu dillaliliya mai saida kwanika. Sai dai kuma kama da wane akace bata wane, dan haka ku maza ku garzaya ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE. domin samun naku kuma. Suna kawo kaya daga ƙasashen ƙetare akan farashi mai sauƙi da rahusa. Suna order ɗin products kamarsu, dukan kayan kitchen na zamani, bedsheets, shoes dade sauransu, products ɗinsu pre-order ne dake zuwa akan lokaci batare da mai kaya ya ƙosa da jira ba ko samun matsala. Zaku iya samunsu a Number waya kamar haka ko Location nasu. Phone number: 08102393622. Location Gombe. Amma Zasu iya turawa kowani gari dake a lungu da saƙo na ƙasarnan. Sayen nagari maida kuɗi gida. Ku garzaya kar ayi babu ku. Da ƙyar nasha yafi da ƙyar aka kamani inji masu iya magana😉😘😘😍😋._* ___________________    ................Kamar bazata juyaba sai zuciyarta ta bata shawarar juyawa taga wane shahararran ƙwallan mara imanine da mutuncine shiɗin,        Abun mamaki babu kowa a wajen,  sai dai an sauke glass ɗin motar kaɗan alamar tanan koma wanene ya isar da saƙon nashi. Jitai zuciyarta ta sake hawa sama fiye da da. Ta yunƙura da nufin nufar motar gayun nan suka sake mata zobe. Kallonsu tai sama da ƙasa a wulaƙance da faɗin, “Wlhy idan baku matsamin ba ɗaya bayan ɗaya saina muku fashin goshi da dutsen nan”.     Babu wanda ya motsa a cikinsu, da alama ma basa fahimtar yaren datai maganar, dan kallonta kawai suke tamkar wasu zakaru. Dutsenta da har yanzu ke a hannu ta sake ɗagawa zata bugama wani again. Da sauri yay baya da ɗana kunamar bindigarsa yana huci. Nu'aymah ta taɓe baki tamkar bata fahimci abinda yake shirin yiba, ta sake ɗaga dutsenta ta makama na gefen hannun haggunta a goshi cikin rashin tsamanin hakan daga garesa.      Ƙara ya saki da duƙewa ƙasa bindigarsa na faɗuwa dan abun yazo masa a bazata, babu yanda za'ay kai tunanin shiɗin zata bugamawa. Ƙafa ɗaya daga ciki ya saka ya taɗeta tai baya zata faɗi cikin security ɗin gidan marayun da suka iso yanzun wajen yay saurin tareta. Ai tanajin bata kai ƙasaba tai wani irin ɗagowa da sauri ta wulwula dutsin nata sai akan motarnan dai ta ɗazun data fasama glass, kuma a gaba ya sauka, dan haka glass ɗin ya ƙara tsatstsagewa fiye da ɗazun.          A yanzunkam bodyguards ɗinsa sun tabbatar bazasu iya haƙura da tsagerancin yarinyarnanba, sai sun ɗauki mataki duk da ogansu bai basu damar yin hakan ba. Hannu ɗaya daga ciki ya ɗaga zai kwasheta da mari iya ƙarfinsa, sai dai ganin za'a buɗe ƙofar motar ne ya sakashi dakatawa da nufar motar da sauri ya ƙarasa buɗewa yana saurin cewa, “Sorry Sir”..            Banji an amsashi ba, sai dai motsin da naga anyi daga cikin motar ya bani tabbacin wanda ke a ciki zai fitone. Ba Nu'aymah kaɗai ba, harsu Yusrah sun zuba idone suga mai fitowar.         Ƙafarsa dake cikin baƙin takalmi mai shegen ƙyau ta fara bayyana, kafin farin wandonsa. A hankali ya dire sandarsa ƙasa itama tare da ɗayar ƙafarsa ya fito gaba ɗayansa.      Koni mai ɗaukar rahoto saida na furta ‘masha ALLAH’ a zuciyata. Zuƙar iskar yammaci data fara kaɗawa yay a hankali cikin hancinsa ya fesar yana sake tamke farar fuskarsa dake zagaye da baƙin gashin saje siɗik, dan a rayuwarsa ya tsani kallo. Baiko kalli ko sashen dasu Nu'aymah da guards ɗinsa sukeba ya nufi inda su Nanah suka rufu kan yaron tare da securitys ɗin gidan marayun. Hannun Malika dake a saitinsa ya kama ya matsar da ita gefe, hakanne ya sakasu farga da isowarsa duk suka dawo cikin hankalinsu daga kallon ƙurullar da suke masa. Baice dasu uffanba yay wani ɗan dirƙuson gayu gaban yaron tare da kai yatsunsa biyu saitin hancinsa, yakai kusan sakan goma kafin ya janye, sai kuma ya maida kan jijiyar wuyansa dake a saitin kunne. Nanma ya kwashe sakan goma da ɗoriya sannan ya ɗauke. Miƙewa yay tsaye, idanunsa dake cikin baƙin glasess akan ƙaton symbol ɗin da aka rubuta sunan gidan marayun, kafin ya janye ya maida dubansa ga guards ɗinsa da har yanzu suke zagaye da Nu'aymah kamar wata ɓarauniyarsu. Da hannu yay musu nunin su barta, tare da yin wani salo da yatsunsa biyu wanda shi da su ne kawai sukasan ma'anar yaran nasa.     Cike da takaicin rashin ɗaukar mataki a kanta sukaja baya kowanne na zuba mata harara a ƙasan ido da huro hanci. Gaba ɗayansu garesa suka nufo. Ɗaya daga ciki ya matso sosai inda yake, A hankali ya furta maganar da babu wanda ya iya jinta a cikinsu Nu'aymah, dan kuwa jajayen laɓɓansa ne kawai suka motsa kaɗan.  Ganin haka ya saka Nu'aymah nufosu da sauri itama. Yana ɗaga ƙafarsa zai bar wajen tana isowa tasha gabansa.       “Kai malam dakata mana! Shin babu zuciyane a ƙirjinka kokuwa kana tunani da zuciyar takane bada ƙwaƙwalwa ba?”.         Kallonta yake daga sama har ƙasa ta cikin glasess ɗinsa, batare da yama nuna alamar ya fahimci yaren da take maganar da shiba ya raɓata zai wuce abinsa. Hanzarin riƙo sandarsa tai ƙoƙarin yi Yusrah ta riƙeta. Cikin magana raɗa-raɗa tace, “Aymah calm down Please, kalla kiga”.        Sai da ta zubama bayansa harara kafin ta kalli abinda Yusrah ke nuna mata. Securitys ɗin gidan marayun ne tare da guards ɗin nasa uku dasu Nanah ta hango harsun kusa shigewa cikin Orphanage ɗin ɗauke da yaron a hannun ɗaya daga cikin guards ɗinsa. Juyawa tai da sauri ta kalli inda yake shima sai ganin motocin uku tai har sunyi reverse suma da alama gidan marayun zasu shiga.              “Zuciyarki tayi sanyi ko? Iya masifa! ALLAH wataran sai kinsa an maidamu kwalta Nu'aymah, jibesu tamkar wasu bajiman zakuna su da ogan nasu. Da ganinsu kasan ba hausawa baneba ma, ke koma tsoro baƙyaji”.         “Mtsoww! Ina ruwana da rashin kasancewarsu Hausawa, inda banyi musu hakanba ai guduwa zasuyi dan tsabar rashin sanin darajar ɗan adam. Ko dabba suka bige ai ta cancanci su fito suga lafiyarta balle mutum, shegu masu suffar baƙaƙen aljanu”.       Dariya Yusrah ta kwashe da ita tana faɗin, “Amma dai banda wannan Handsome ogan nasu ko? Dan wlhy dai kam komai yaji zammm anan kema kin sani”.         “Ke kikaga wannan”. Nu'aymah ta bata amsa tana fisge hannunta dake cikin na Yusrahn ta tsallaka titi ta barta tana dariya. Dan ta kula bori kawai Nu'aymah keyi itama tasan gayen ya haɗu masha ALLAH, sai dai yanayinsa sam bai mata kama dana Musulmai ba, dan askin kansa kawai da ƙaton sarƙan Cross na diamond dake a wuyansa, da ɗan kunne guda ɗaya manne a kunnensa ya isa amsar hakan a garesu.       Hango Nu'aymah har zata shige cikin Orphanage ya sakata saurin tsallaka titin itama ganin babu mota tabi bayanta.        Nu'aymah da har yanzu keta faman jan tsakin takaicin mutanen ta nufi clinic ɗin gidan kanta tsaye, tasan dai bazai wuce can suka nufa da yaron ba. Kasancewar tafiyar tata sai a hankali, ba wani sauri ta iyaba kuma akwai tazara tsakanin gate ɗinma da clinic ɗin saiga Yusrah harta isketa. A tare suka ƙarasa batare data kula Yusrah daketa son taga ta sakko ba. Tsaitsaye suka iske su Nanah a reception da guards ɗin mutumin, sai bah-bah hindatu ɗaya daga cikin masu kula da yaran, da kuma Abban Adawiya da ashe tun ɗazun yana a cikin gidan marayun su Nu'aymah basu saniba.       Waige-waigen inda zataga gayen ta farayi, sai dai babu ko mai kama da shi a wajen. Wani takaicine ya sake dirar mata a zuciya, cikin ranta ta ayyana ‘Wato shi yamafi ƙarfin shigowa kenan? To ai idan yasan wata baisan wataba’. Ta nufi hanyar fita tana surutunta a zuciya.      Yusrah da tunaninta ya bata Nu'aymah zata iya zuwa ta sakemusu ɓarna a motoci tai saurin riƙo hannunta tana faɗin, “Ina kuma zakije?”.           “Yusrah sakeni, bakiga wannan mai shegen taurin kan bai biyosu ba”. “Oh ALLAH, to minene idan bai shigo ɗinba, baga guards ɗinsaba, nasan ai zasu wakilcesa. Ki tunafa ba shine ya buge yaron ba ma, cikin guards ɗin nasane tunda shi yana a motar tsakkiyane, sannan ba shinefa ke tuƙinba”.          “Wannan matsalarsace kuma, ai wanda ya bige ɗin dai yaronsane ko? To ya zama dole shina ya kasance a wajen wlhy dan ya ja masa matsala”.        Kafin Yusrah ta samu damar mata magana sai gashi ya fito daga ɗaya a cikin ɗakunan clinic ɗin, Dr Safwan biye da shi a baya, taku yake cike da nutsuwa irinta zaratan samari masuji da lokacin ƙuruciya da kwanciyar hankali. Handglop ɗin dake a hannunsa taga yana zarewa ya jefa cikin shara. Har yanzun dai idanun nasa a toshe suke da Google ɗin, kuma fuskar a tamke, tana ƙoƙarin janye idanunta daga kallon nasa caraf suka sauka bisa kan ƙatuwar sarƙar Cross ɗinsa da aɗazun masifa baisa ta ganta ba.       Cikin suɓutar baki tace, “Ashe Arne ne shiyyasa baida imani”.      Karaf wannan magana a kunnensa. Sai dai yanza yazo ya gittata ya barta da ƙamshin turarensa mai sanyin daɗi batarr da ko kallon inda takeba ne, zaka fahimci da wahala ace yamaji mitace, maybe ma bayajin hausar sam.           Wajen Abbah dake zaune ya ƙarasa, suna ɗan nesa dasu kaɗan shiyyasa bazasu iya jin mi suke faɗa ba. Ta taɓe baki da nufar Dr Safwan tana tambayarsa yaya jikin yaron?.        “Jikinsa Alhmdllh, ai bama wani ciwo yaji sosai ba, yadai bugune a kansa da hannunsa na haggu, insha ALLAH kuma fatan komai zaiyi normal da wuri”.       Duk da taji daɗin hakan sai bataji ranta ya huce daga haushin mutuminda ita kanta shaidace tasan ba shine ya aikata laifin ba. ‘Amma kuma ai ogan wanda ya aikata ɗinne’ ta raya a cikin ranta cike da gamsuwa da jawabin zuciyarta.          Ɗakin da yaron yake kwance suka nufa suka dubashi duk da ansa masa ruwa barci ya ɗaukesa. Lokacin da suka fito basu iske mutanenba har motocinsu. Hakan ya bama Nu'aymah tabbacin sun wuce kenan.          Suma nufar hostel ɗin yaran sukai suna sake tattauna abinda ya faru, tare da yin gulmar mutumin dako sunansa basu saniba. Nu'aymah dai uffan bata cewa, dan ita takaicima suke ƙara mata a kanshi kawai.                          ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka karanta idan baka biyaba, karka kuma yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 _______________________         Tunda suka baro cikin Orphanage ɗin ya kwantar da kansa jikin kujera yay shiru idanunsa dake da cikar baƙin gashi da gira a sama suna a lumshe. Sai faman juya glasess ɗinsa dake a hannunsa na dama yake tamkar zai karyasa. Gaba ɗaya abinda ya farune ke dawo masa cikin zuciya daki-daki. Ya yarda yaran Arewan nan basajin magana tamkar yanda yakeji ana shan faɗa. Jibafa yanda ƴar yarinya ƙarama sa'ar ƙanwarsa Victoria ta tsaya agaban bindiga tana musu raini tamkar wasu sa'anninta. A karan farko yaja ƙaramin tsaki da furzar da iskar daya cika baki da ita yana maijin takaicin komai a ransa. A hankali ya buɗe idanunsa ya kai dubansa ga glass ɗin gaban motar tasa da Papansa yasa maƙudan kuɗi wajen siya masa. Yau shine hawansa na farko da motarma gaba ɗaya, dan sati biyu da suka wuce papa ya bashi ita a birthday ɗinsa matsayin gift. Amma sai gashi cikin sakanni an mata walmakalifatu, kamar Mom tasan hakan zai faru tace bata yarda yazo kano a mota ba daga Abuja, shi kuma gashi yanada uzirin da bazai yuwu ya fasa tafiyarba, dan dama zaibi jirgine kamar yanda ya saba sai akace jirgi bazai tashiba dan yanayi babu ƙyau yau. Shinefa ya zaɓi tahowa a mota duk da Mom bataso hakanba. Sake rumtse idanunsa yay da shegen ƙarfi da cije lip ɗinsa na ƙasa sosai tamkar zai hudashi da haƙori.         Duk abinda ya keyi drivernsa na kula ta cikin mirror, hakanne ya saka zuciyarsa sake zafafa da abinda yarinyar tai musu shima, ya kai hannu ya shafa inda Nu'aymah tai masa rotse da dutse aka saka masa bandage, wlhy yau badan oga ya hanasu ba da yarinyarnan saidai uwarta ta haifa wata. Shiyyasa shifa a rayuwarsa yay mugun tsanar ƴan Arewa ɗin nan musamman hausawa, ƙauyawa dasu ko karatu basayi sai rashin mutunci. (Humm malam driver naka tunanin kenan, amma ƴan Arewa sun wuce da sanin duk wani gurɓataccen tunaninka ai🙄😏). Shi yanzu babban tashin hankalinsa ma mi zasuce da Madam ɗinsu akan wannan al'amarin daya faru?, dan kowa yasan yanda family ɗin gaba ɗaya ke masifar so da ƙaunar ogan nasu tamkar wani tsoka ɗaya a miya.       Haka dai suka cigaba da tafiya kowa da abinda yake saƙawa a cikin rai. Gashi mahaukacin gudu sukeyi kai kace Lagos suka nufa ba Abuja ba.        Tunda 6pm tayi kiran Mom ya fara shigowa a wayarsa, sai dai ko sau ɗaya bai amsa mataba ya share, sai ma kwanciya daya gyara cikin lallausar kujerar motar ya cigaba da latse-latsen laptop ɗinsa har yanzu da takaicin Nu'aymah a ransa. *_ABUJA_*           *_09:30pm_*  Dai-dai suka shiga garin Abuja saboda holdup daya riƙesu a madalla zuwa Kubwa expres, da ƙyar suka fita a jigace, dan kafin su iso Asokoro ji yay tamjar ya fasa ihu dan gajiya, shi dama can mutum ne da baida jimirin tafiya mai nisa a mota, duk da tafiye-tafiye sun kasance cikin ginshiƙin aikinsa kuwa.          Anguwace da bata da maraba da a cikin turai saboda rashin hayaniya da haɗuwarta. Ko ina ƙwanyar yake da wutar nepa tamkar rana, duk da dare baiyi nisaba babu abinda kakeji sai haushin karnuka. Motocin uku suka tsaya dai-dai saitin wani ƙaton baƙin gate da zaka iya hango cikin gidan daga waje kasancewarsa tamkar net. Horn sukai, da gudu sai ga wani dake cikin Blue Uniform ya iso da sauri ya buɗe musu.      Tunkan su gama dai-daita parking idanunsu suka sauka akan Madam Chioma dake ta faman kai kawo ta barandar saman bene. Sai dai ganin shigowar motocin tuni tabar wajen da alama zata fitone.        Tuni Securitys ɗin gidan kusan su goma sha biyar suma sukayoma motar caaa. Buɗe masa akai da sauri, sai dai kafin ya fito Madam Chioma harta iso. Da kanta tasa hannu ta fiddosa a motar, tai saurin rungumesa tana magana cikin yarensu. “Yarona miya sameka? Ina kuka tsaya? Miyasa kaki ɗaga kiranmu?”. tashiga jero masa tambayoyin batare data bashi damar amsa ko guda ɗaya ba daga ciki.            “Relax Maa! i'm okay”. “Ka tabbatar?”. Ta faɗa tana ɗagosa daga jikinta hannayenta duka biyu akan kwantaccen sajensa tana shafawa, sai kuma tabi jikinsa da kallo daga sama har ƙasa. Ganinsa dai lafiya lau saita sake rungumesa tana faɗin, “Thanks God”.            “Ɗan uwa sannu da zuwa”. Wata murya ta faɗa daga bayansu cikin harshen nasara. Sakinsa Madam Chioma tai suka juya suna kallon mai maganar. Matashin saurayine da bazai wuce 22years ba, sai kuma wasu dake bayansa su kusan bakwai. Kallonsu yay ɗaya bayan ɗaya kafin ya buɗe masu hannayensa sukazo duk suka rungumesa suma suna masa sannu da zuwan. Sai da duk suka gama sannan ya amsa musu da “Thanks you”. a jimlace.       Har sun nufi babbar ƙofar shiga ainahin cikin gidan ɗaya daga cikin yaran cikin harshen turanci tace, “Jesus!! Miya faru da motarka Brother?!”.      A tare duk suka juya suna kallon motar, amma banda shi dama yay gaba abinsa tamkar baiji mi Joy ɗin ta faɗa ba.        Cike da firgici Madam Chioma ta shiga ƙwala kiran sunan guards ɗinsa ɗaya bayan ɗaya. Aiko jikinsu har rawa yake suka nufota ransu cike da tsoron amsar da zasu bata akan abinda sukasan dole su amsa tambayoyinsa dama.           Aiko a jajjere ta shiga jero musu tambayoyin ko bari su bada amsa batayi. Sai da ɗaya a cikin yaran da zatama iya kai sa'ansa tace, “Mom ki shiru haka mana su bamu amsar miya faru?”. Zata sake magana budurwar tai saurin sake faɗin, “Please Mom”. Shiru tayi badan taso hakanba. Ta maida hankali ga guards ɗin da saima yanzune ta kula da masu fasashshen goshi biyu a cikinsu. Babban ne ya shiga mata bayanin duk abinda ya faru tsakanunsu dasu Nu'aymah daga farko har ƙarshe. A take takaici da baƙin ciki suka sake rufeta ta shiga zagin Hausawa da kiransu da sunaye marasa daɗin ji. Sai da tayi iya iyawarta kafin ta bar wajen tabi bayansa. Suma sauran yaran bayan nata sukabi suna zagi.         Shikam yana shiga ƙaton babban falon gidan dake ɗauke da set ɗin kujeru biyu mabanbanta kala baiko tsaya ba yay saurin hayewa sama inda sashensa yake. Baya buƙatar kowa ya biyosa, dan haka yay saurin maida ƙofar corridor ɗin sashen nasa ya rufe, sannan ya ƙarasa nasa madaidaicin falon daya gama haɗuwa, yanata wani tattausan ƙamshi mai daɗin shaƙa da kwantar da zuciya. murza ma ƙifar falon key yayi sau biyu sannan ya shige. dispencer dake acan gefen dining mai ɗauke da madaidaicin d/table ya nufa, ya ɗauki glass cup dake cikin wani showglass mai ƙyau da ɗaukar hankali ya matsi ruwa. Tas ya shanye wanda ya ɗiban, ya ajiye kofin saman d/table ɗin ya baro wajen zuwa wata ƙofa dake a cikin falon. Nan ɗinma dai corridor ne, sai dai ƙofa biyu ce kawai a cikinsa, ƙofar ƙarshe ya nufa yana zame baƙar jacket ɗin jinsa tunkan ya buɗe. Ya riƙeta a hannu ɗaya sannan ya ƙarasa ya murda handle ɗin ƙofar ya tura ya shiga.        Fes ɗakin yake shima, yanata tashin ƙamshin fresheners data haɗe da turaren da yake amfani da shi. Jefa jacket ɗin yay saman gadon ya ƙarasa gaban mirror yana ƙoƙarin cire sarƙar cross ɗin wuyansa. Ya ratayeta jikin wani ɗan hangar ƙarami mai ƙyau dake cike da sarƙoƙin kala-kala a  ajiye saman mirrorn. Zama yay a stool ɗin gaban madubin yanata faman yamutse fuska dan yunwa yakeji, sai da ya cire takalman ƙafarsa da safar, farar ƙafarsa dake fes ta bayyana kafin ya miƙe kansa tsaye ya nufi wata ƙofar da ko ba'a faɗaba kasan toilet ne.      Yana shiga aka fara knocking ƙofar falonsa, amma sai ya share ya cigaba da abinda yake a ciki. Anyi kusan sau uku sannan aka bari. Ya ɗauki tsahon lokaci a bayin kafin ya fito sanye da bathrobe Milk color. Hannunsa riƙe da ƙaramin towel yana tsane sumar kansa da kallo ɗaya zakai mata ka fahimci tana masifar lasar kuɗaɗe kodan ƙyawun da take dashi ga mai kallo a ido balle kuma wanda ya taɓa.          “Yoohan! Buɗe min ƙofa”. Ya tsinkayo muryar Mom tana faɗa cikin yarensu da ɗan buga ƙofar yanda tasan bazai takurasa ba. Gefe ya karyar da wuyansa yana yamutsa fuska da yarfar da hannayensa duka alamar shifa an takura masa. Fuskarsa cike da takaici yaje ya buɗe mata tare da juyowa a binsa batare da ya tsaya saurarenta ba.      Ƴar dariya tayi abinta, dan ko kaɗan hakan bai dametaba, tasan ya gajine matuƙa, shikuma idan ya gaji to lallai sannan baƙin ransa ke ƙara hauhawa, kowa kuma yimawa yakeyi har ita da Papa. Ƙarasawa tai inda yake tsaye a gaban mirror yana cigaba da tsane kansa. Kama hannunsa tai ta zaunar, ta amshi towel ɗin ta cigaba da goge masa kan tana kallonsa ta cikin mirror fuskarta washe da murmushi.      Shiko ya ciskule tasa kamar zai fasa ihu. Sai da ta tsane masa kan tas kafin tajawo hand dryer ta jona a jikin soket ta fara busar masa da shi. Ajiye dryer ɗin tayi da jan hancinsa tana faɗin, “Nasan wannan fushin bana komai bane sai yunwa da gajiya my boy. Taso kaje kaci abinci ka kwanta ka huta”. Tai maganar da turanci           Yana shirin miƙewa danya shirya akai knocking ƙofar, jiyay tamkar ya fasa ihu dan takaici, shiyyasa sam bayason zaman gidan nan wani lokacin, dan ana hanama rayuwarsa shaƙatawa da hutawa. A hakanma gwara nan, abinda yafi tsana shine zuwa ƙauyensu, dan anfi cika masa ciki da takaici acan fiyema da nan Abuja. Mom ce tai magana, shiko tuni ya miƙe ya koma wajen kayansa. Ɗaya daga cikin ƙannensa ce mai suna Victoria. Tarkacen kayansa ne daya bari a mota cikin guards nasa ya kawo tun ɗazun, shine yayta masa knocking lokacin daya shiga bayi, da yaji ba'a buɗeba ya koma dasu ya bama yaran akan idan ya fito saisu kawo masa.           Zubesu tai akan table ɗin gaban gadon, ta juya garesa zatai magana ya ɗaga mata hannu da sauri tare da nuna mata ƙofar fita. Baki ta kumbura ta juya ta kalli Mom nasu dake murmushi sannan ta fice tana buga ƙafafu da ƙananun kukan taɓara.       Miƙewa Madam Chioma tayi itama tana faɗin, “Ina jiranka kai maza ka fito”. Kansa kawai ya ɗaga mata ya cigaba da abinda yakeyi...........✍ Read more har bakwai yau?.😳😵😓🚶🏻. _____________________ SAHFAT PREORDER! ______________________         Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗. SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya. Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske. *_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._* _To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_. Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU. Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa. *_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_* _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻[4/7, 10:56 AM] Amina Mama: ________________________ *ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*        *_KAJI shahararrun kuma mandiyoyin ƴan ƙwalisar kawo kayan kitchen masu tafiya dai-dai da zamani. Idan nace nadaban ina nufin suɗin nadabanne wajen kaya ƴan gaske dake ƙawata kitchen ɗin amarya harma dana uwargida ƴar ƙwalisa. Ka siya ka tabbatar ka saya ɗin ko a gaban tsaranka sai ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE. sunan kayansu sa kishiya cin bashi🤣, dan tana ƙyalla ido taga kitchen ɗinki tsarin amerikawa tuni zata fara ƙwafa da tunanin zuwa gidan delu dillaliliya mai saida kwanika. Sai dai kuma kama da wane akace bata wane, dan haka ku maza ku garzaya ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE. domin samun naku kuma. Suna kawo kaya daga ƙasashen ƙetare akan farashi mai sauƙi da rahusa. Suna order ɗin products kamarsu, dukan kayan kitchen na zamani, bedsheets, shoes dade sauransu, products ɗinsu pre-order ne dake zuwa akan lokaci batare da mai kaya ya ƙosa da jira ba ko samun matsala. Zaku iya samunsu a Number waya kamar haka ko Location nasu. Phone number: 08102393622. Location Gombe. Amma Zasu iya turawa kowani gari dake a lungu da saƙo na ƙasarnan. Sayen nagari maida kuɗi gida. Ku garzaya kar ayi babu ku. Da ƙyar nasha yafi da ƙyar aka kamani inji masu iya magana😉😘😘😍😋._* _______________________________ 14 .................A tare suka fito harabar gidan, inda suka iske matan gidan da sauran samarin da basu kai ga ficewa sabgoginsu ba duk sun fito suma.       Suna ƙarasawa ga ƴan sandan Nu'aymah da Amal taje ta kira itama sai gata ta fito tana ɗan ɗingisa ƙafa. Sanye take da siket da riga na atanfa, sai ƙaramin hijjab da Umm ta sabar mata da sakawa a cikin gidan saboda samarin gidan tunda ba muharramanta bane ba.        Tunda su Baba malam suka fito jikin wasu a cikin police ɗin yayi sanyi ganin dai da gaske an turosune gida mai daraja kamar wannan dan suyi abinda basu da tabbacin faruwarsa tunda ba'a gabansu akaiba. To amma yaya zasuyi, d.p.o ne da kansa ya sakasu zuwa su kama Nu'aymah, ga kuma kuɗaɗe da sukaci har kashi biyu daga Papa da kuma guards ɗin Yoohan na toshiyar baki. (Ya rabbi ka tsaremu cin rashawa da bada ita. Amin🙏🏻😭).              Sun gaisa dasu Abba cikin girmamawa, kafin su sanar musu daga station ɗin da aka turosu da kuma abinda zasuyi. Kusan a tare su Abbah duk suka juya suna kallon Nu'aymah. Baba malam ne kawai kansa a ƙasa yana ɗan murmushi. Batare da yace komaiba ya nufi inda jama'ar gidan ke tsaitsaye suma suna kallonsu hankali a tashe.        Hannun Nu'aymah ya kama batare da yacema kowa uffanba. Itama kuma babu musu ta bisa har wajen ƴan sandan. Ya miƙama macen hannun Nu'aymah yana faɗin, “Itace wannan?”.         Kallon hoton dake a waya babban nasu yayi, kafin ya kalli Nu'aymah. “Eh itace ALLAH ya gafarta malam”. Ya faɗa cike da girmamawa ga baba malam. Murmushi baba malam yay musu yana nuna masu Nu'aymah dake kallonsa kamar wata sokuwa. “Gata nan, zaku iya tafiya da ita”. Da sauri Abban su Abdallah ya yunƙuro zaiyi magana baba malam ya ɗaga masa hannu fuska a ɗaure. Cak ya tsaya hankalinsa a ƙololuwar tashe. Hakama su Abban Adawiya hankalin nasu a tashe yake da hukuncin da baba malam ya shirin yankewa. A ganinsu ai basai anje station ba, zasu iya tsayawa su tattauna anan, musamman ma shi Abban Adawiya da yana cikin Orphanage randa abin ya faru. Kuma an sanar masa komai akai.         Godiya ƴan sanda sukai tare da juyawa da Nu'aymah zasu tafi. Tirjewa tai tana kallon Baba malam daya ɗauke kansa gaba ɗaya daga garesu tamkar baisan mi akeyiba. Hannunta ta fara ƙoƙarin fisgewa idanunta na cika da ƙwalla. “Abba wlhy bansan mina musu ba”. Tai maganar muryarta na rawa.      Juyawa baba malam yayi zai bar wajen batare daya kula maganar Nu'aymah ba. Sai da yay taku biyu uku sannan ya tsaya tare da juyawa ya kalli ƴan sanda da Nu'aymah data fisge zata dawo. Cikin tsananin kaushin murya yace, “Idan bazata biku da arziƙiba ku ɗauketa!!”.       Tsayawa Nu'aymah tayi cak tana kallon baba malam ɗin. Sai kuma ta kalli inda su Umm suke. Sake dawo da idonta tayi kan ƴan sandan da suma ita suke kallo. kunyar baba malam ce kawai ta hanasu fara cin ƙaniyarta tun anan. Tsaf ta haɗiye kukanta. Ta juya cikin ɗingishi ta nufi ƴan sandan. Basuce mata komaiba suka tasa ƙeyarta gaba suka fita waje inda motarsu take.       A gaban ƴan anguwa daketa kai kawo aka sakata a motar ƴan sanda. Gaba ɗaya hawayen da Nu'aymah ta fara ɗazun sun ƙame ƙaf. Ta cusa kanta tsakanin cinyoyinta tai shiru. Sai faman cije baki kawai take saboda zugi da ƙafarta ke mata. Har suka isa police station ɗin bata ɗagoba. Sai da ƴar sandar ma ta taɓata sannan ta san sun iso. Ɗago kanta tai a hankali ta kalli station ɗin, sai kuma ta juya ga ƴar sandar dake mata kallon tausayi. Dan ita yanda taga mutanen na hanƙoro akan yarinyar ta zata ma wata tsohuwar macece, ashe yarinyace ƙarama. Itace ta taimaka mata ta fito, ta kama hannunta ganin kamarma ta kasa tsaiwa. A haka suka shiga cikin station ɗin da taimakon ƴar sandar.            “Amma Yaya ka.......” hannu baba malam yay saurin ɗagama Abban su Adawiya dake son masa bayanin ainahin abinda ya faru. Ya kallesa fuskarsa babu wasa, “Banason jin komai akan hakan Mustapha. Kaje ka shirya mu wuce banason yazam mu ake jira”.      Kai kawai Abban su Adawiya ya kaɗa masa. Kafin ya kalli su Abba Musbahu ya bar wajan jiki a sanyaye. Da sauri su Abban Abdallah suka nufi mota da nufin bin bayan su Nu'aymah, sai kawai a bazata suka tsinkayi muryar Baba malam na faɗin, “Na haramtawa kowa bin bayanta a cikin gidan nan, idan kuma wani ya aikata koda ban saniba zai fuskanci fushina”.      Cak suka tsaya daga yunƙurin shiga motar, kowannensu goshinsa na tara zufa. Babu wanda ya iya sake cewa komai har Baba malam ya shiga sashensu ya fito cikin shirin fita. Ta gabansu ya wuce zuwa sashen Hajjo data sha maganin mura tun ɗazun ta kwanta. Duk wainar da ake toyawa bata saniba dan barci takeyi. Baifi mintuna biyarba sai gashi ya fito.  Yanzunma bai kalli sashen da kowa yake ba ya nufi inda motar da zasu tafi take, sauran motocin uku da ɗalibansu zasu shiga da ƴan agaji kuma duk suna a harabar massallaci.      Suna kallo motar ta fice batare da ko mutum ɗaya ya iya cemasa a dawo lafiya ba, shima kuma bai nuna ya damu da hakan ko jiran cewar tasu ba.       Umm ce ta fara sulalewa ta koma ciki, kafin sauran suma su fara zare jiki ɗai-ɗai suna shigewa sashensu. Addah dai bayan Umm tabi tana share hawayen da ke sakko mata batare data farga da fitowarsu a cikin idanunta ba. _____________ *_ABUJA_*         Tunda labarin kama Nu'aymah ya isa kunne Papa farin ciki ya mamayesa shi da Madam Chioma, breakfast da suke shirin zamanyi ma su kasawa sukayi, sai kai kawo sukeyi zuciyoyinsu fes kamar an basu rabin duniya.     Dolene yasa a koyama yarinyar hausawan nan hankali, dan shi a rayuwarsa idan da abinda yafi tsana a rayuwarsa to ƴan yankinta ne. Ya tsani yarenta fiye da mutuwarsa, a cewarsa babu abinda suka iya sai haihuwa, ƴaƴan nasu kuma babu tarbiyya sam, daga ƴan bangar siyasa sai masu bara. Sam mutanen da yankinsu basu masaba, inda ace zai iya zama shugaba, sai ya shafe yankin ko tarihinsu baza'a sake aji ba. (hummm Papa, a ringa sara dai ana duban bakin gatari).            Abinda papa ya keta faman rayawa a ransa kenan yana murmushi. Waya ya sake ɗagawa yay magana da d.p.o ɗin akan yanzunan a bama guards ɗin Nu'aymah su taho masa da ita Abuja. Shi kuma d.p.o ya turo da accaunt Number ɗinsa yanzu zaiji alert.         Cike da farin ciki d.p.o ya amsama papa. Babu ko tunanin komai a ransa ya aika da accaunt details nashi, ya kumayi zaman shirya takardar ƙarya akan laifin da bashi Nu'aymah ta aikataba. (Humm! Ya ALLAH ka shiryemu ka shiryi shuwagabannin mu da jami'anmu. Ka tsame bara gurbin cikinmu, idan masu shiryuwane ka shiryesu. Idan bazasu shiryuba UBANGIJI kafimu sanin miya dace dasu, mun barka dasu😭🙏🏻). ________________ *_LAGOS_*          Fitowarsa kenan daga ɗakin theatre a matuƙar gajiye. yanda yake tafiya kawai zai baka wannan amsar. Tare yake da likitoci uku da suka tayasa aikin, sai Nurses suma guda uku. Dai-dai sun ƙaraso ƙofar wani office nurse ɗin dake a gefen damarsa ta miƙa masa tasar hannunta ya jefa hand gloves ɗin daya cire daga hannunsa ya jefa a ciki, hannu ya ɗaga musu kawai alamar su dakata anan ya tura ƙofar ya shige.        Basu damu ba, dan kowa yasan Dr Yoohan haka yake, mutum ne mai ƙoƙari akan aikinsa da himma, ga tausayi sosai musamman ga marasa ƙarfi. Bashi da yawan magana, sannan baida fara'a. Wanda bai fahimcesa ba zaita ɗauka kamar kullum shi cikin ƙuncin rayuwa yake, kokuma girman kaine bisa ga ɗaukakar da ALLAH ya basa. Idan kuma ka fahimcesa zaka gane cewa haka halayyarsa take, shi kawai aikinne a gabansa ba shiririta da shashanci ba. Akance likitoci mafiya yawansu sunada son mata, sai dai ga Dr Yoohan sam ba haka baneba. Duk yanda matan ke binsa da soyayya shi bama su ishesa kalloba, shi fa a rayuwarsa damuwarsa kawai shine aikinsa, sai ko family ɗinsa da taimakon marasa ƙarfi. Idan ya shiga cikin musulmi bazaka taɓa cewa shi ba musulmin bane, musamman daya ajiye ƙasunba da yanda yake gudanar da al'amuransa sak halayyar musulman ƙwarai. Sai dai fa idan kaci karoda sarƙar Cross a wuyansa da akoda yaushe baya fashin sakawa ne zaka gane daga ina ya fito. ALLAH ya ɗaukakashi a duniya a dalilin ƙwaƙwalwar aikin likitanci daya azurtashi da ita, likitane shi da kota wane fanni zai iya gunar da aikinsa akan mara lafiya, sai dai abinda ba'a rasaba kam, dan UBANGIJI shine mai komai da kowa.          Office ne daya amsa sunansa office. Bakajin komai sai sassanyan ƙamshin turarensa dana ac. Wanda ke zaune a rikunin kujeru uku dake can gefen office ɗin yana aiki ya miƙe yana masa barka da fitowa cike da kukawa.      Kansa ya ɗaga masa fuska a yamutse na alamar gajiya. kafin ya ƙarasa ga kujerar zamansa yaja wani file dake a jiye ya fara singing.       Tasowa Richard yay da sauri garesa yana murmushi, ya ajiye files ɗin hannunsa gaban Dr Yoohan ɗin yana faɗin, “Doctor akwai mutane biyu da zaka ganifa yanzun kafin ka tafi hutun awa uku da rabi, idan lokaci ya cika zaka sake shiga theatre room, na mutane biyu da suka rage suma”. Da sauri Yoohan ya ɗago yana kallon Richard fuska a marairaice kamar zai fasa kuka. Richard yay saurin haɗiye dariyar dake neman kufce masa dan yasan shima da gaske Yoohan ɗin ya kai iyakar gajiya, amma sai ya fiske yace, “Da gaske nake Yoohan, gama files nasu na kammala dubawa”.           “Rich.. Please, wlhy na gaji, sai dai kai ka dubasu” ya faɗa yana sauke numfashi da miƙewa ya nufi wata ƙofa.       Murmushi Richard yayi yana binsa da kallo harya shige. Ya ɗan girgiza kansa da kwasar files ɗin ya fice daga office ɗin zuwa nashi shima.          ALLAH ne ya haɗashi da Yoohan tun a secondary school, a farkon haɗuwarsu sam basa shiri, dan abokan faɗan junane a aji. Ba komai yasa rashin jituwa tsakaninsu ba sai kasancewar su duka sunada matuƙar ƙoƙari, kafin Yoohan yazo school ɗin shike ɗaukar na ɗaya a ajinsu, amma Yoohan na zuwa ya amshe wannan matsayin. Kafin zuwan Yoohan ɗin kuma kowa sonsa da girmamasa yake a ajin, hasalima shine Monitor, ƴammatan ajin ji suke tamkar su haɗiyesa kuma. Amma Yoohan na zuwa nanma komai ya canja, kan ƴan ajin ya rabu biyu, wasu na ɓangaren Yoohan wasu Richard. Dan haka aka zama abokan dabin juna, duk da sam Yoohan baya kula duk haukarsu. Rashin kulawar Yoohan ɗin tasa a koda yaushe shi da tawagarsa suke ɗauka Yoohan matsoracine, dan babu wanda ya taɓa ganin faɗansa. Sai fa wataran da suka kaishi bango yayma Rich dukan mutuwa, da ƙyar aka karɓesa a hannunsa dan Yoohan akwai zuciyar tsiya. Tun daga wannan duka da Yoohan ya masa suka koma abokan juna, tun sauran ɗalibai na ƙalubalantar abotar tasu har suka fahimci ta gaskiyace suma sukabi. Shi da Yoohan duk burinsu ɗaya ne akan karatu, dan haka haɗewarsu waje guda ta ƙara musu himma da ƙwazo. Koda suka kammala secondary kuma cikin amincin ALLAH iyayensu suka amince musu tafiya karatu tare. A gaba ɗaya rayuwarsu tare ta gudana, sai daga bayane Yoohan daya cigaba da wasu kwasakwasai (Courses) ne suka ɗan rabu, danshi ya amshi aikin da aka bashine a ƙasar London bayan zamowarsu cikakkun likitoci, saɓanin Yoohan daya ƙi amincewa.      Daga baya Yoohan ya kuma samun ɗaukaka fiye da tashi, danshi ya ƙara faɗaɗa wasu karance-karancen daya bashi damar iya duba marasa lafiya ta kowane fanni, aikinsa ya zam zai iya yinsa a kowacce ƙasa kuma.        Bayan shekara ɗaya da fara wannan gwagwarmayar Yoohan ya fahimci bazai iya shi kaɗaiba sai da taimakon Richard, dan haka yaje ya dabaibayesa da daɗin baki har saida ya amince suka sake curewa waje guda suke gudanar da aikin a tare. Yanzu haka shekararsu ta biyu kenan da fara aiki, suna ɗaya daga cikin manyan matasan likitoci da duniya ke alfahari dasu bama ƙasarsu ko yankin Africa kawai ba.     A yanzu haka dai shi Richard ana shirin aurensa ma da wata baturiya, shiko Yoohan yaƙi motsawa sam, a cewarsa shi bama zaiyi aure yanzuba sai nan da wasu shekarun daya tsara.            Ɗakine madaidaici dake ɗauke da kayan ɗaki complete, shima sai ƙamshi yakeyi kamar ba'a cikin asibiti ba. Kansa tsaye toilet ya nufa yana faman lullumshe idanu dan barci yake matuƙar ji. Tunda ya iso Lagos a daren jiya bai hutaba, dan ya iske patients da yawa da sukai booking ɗin ganinsa. Tun a jiyan yay dauriyar zaman duba files ɗinsu, waɗanda yasan akwai mafita ya rubuta musu Doctors ɗin da zasuje su gani ya turama Rich. Waɗanda kuma yasan sai shine zai duba ya sanar da Richard ya sanar musu time ɗin da zasu gansa ta hanyar text messeges.        A safiyar yau tun ƙarfe huɗu na asuba ya baro gida, tunda yazo kuma aiki yake bai hutaba. Bayan ya gama duba adadin daya ƙayyade ya shiga theatre akan matsaloli daban-daban kuma, yanzunma ba ya gama baneba, yanada loacin hutawa ne na awa uku da rabi kafin ya koma ɗakin theatre ya ƙarasama mutane biyu dake a ƙasa kamar yanda Rich ya faɗa. Bayan ya kammala dasu zai ƙara hutun awanni uku jirginsa ya ɗaga zuwa ƙasar Kenya inda wasu patients ɗin ke jiransa canma.             Bayan wasu mintuna ya fito daga toilet ɗin sanye da rigar wanka Blue, sai hular wanka data kare gashinsa daga jiƙewa, da alama dai baya buƙatar jiƙawar. A bakin gadon ya zauna yana mai furzar da iskar daya cika bakinsa da ita, yajawo wayarsa dake a drowar gefen gadon a jiye ya cireta a silent. Dan ya sakata a silent ɗinne tun lokacin dazai shiga theatre room. Solomon ya kira, sai akai rashin sa'a ya samu wayarsa a busy.         Kume fuska ya sakeyi alamar baiso hakanba, ya ajiye wayar. ɗayar ya ɗauka itama ya cireta a plane mode daya sakata. Kamar jira ake ya cire ɗin sai ga kira ya shigo, kafin ya amsa kuma akai knocking ƙofar. Rasa wanne zai farayi yayi. Ɗaga wayar? Kokuwa buɗe ƙofar?.        “Yoohan!” ya tsinkayi muryar Richard na kiransa. Duk da yayi tunanin akan maganar patients ɗin da Rich ɗin yay maganar zai dubane hakan bai hanashi tashi ya buɗe masa ƙofaba, sai dai ya sake haɗe fuska alamar da gaske ya gaji baison takura.       Yana buɗe ƙofar yace, “Rich plea.....”           Saurin katsesa Richard yay da faɗin, “Yi haƙuri ba wancan maganar bane, akwai damuwa Yoohan, matar da kaima aiki a kano yanzun nan Doctor Sa'ad ke sanar min an samu matsala”.        “What?!” ya faɗa hankali tashe. Shima Richard da hankalin nasa ke a tashe ya shiga jinjina masa kai. Juyawa cikin ɗakin yay da sauri, yama manta da wata gajiyarsa. Wayarsa ya ɗauka domin neman Dr Sa'ad. Ganin ashe shinema ya kirasa ɗazun lokacin da Richard ke knocking ya sakashi kiransa. Bugu ɗaya kuwa Dr Sa'ad ɗin ya ɗaga.        Ko gaisuwa basuyi zaman yiba Dr Sa'ad ya shiga masa bayanin dukan abinda ya faru, da halin da matar ke a ciki yanzun.         Hannunsa dafe da kansa cikin tsagwaron damuwa yace,  “Dr Sa'ad ta yaya hakan ta faru? Ince duk yanda ya kamata a bata kulawa na sanar muku. Miyasa kuke da sakaci akan rayukan mutane!!?” ya ƙare maganar da ɗan kaushin murya.         Dr Sa'ad da maganar Dr Yoohan tai masa zafi ya buɗe baki zaiyi magana cikin ƙoƙarin danne fushinsa, amma sai Yoohan ɗin ya kuma dakatar dashi ta hanyar faɗin, “Bana buƙatar jin komai please, zan turo maka hanyar da zakubi wajen fara bata taimako yanzun, nima ina hanyar tahowa”.        “Okay Sir” Dr Sa'ad ya amsa masa daga can cikin wata irin murya mai cike da ɗaci da takaici. Yaro ƙarami dashi yana juyasu dan kawai ALLAH ya basa baiwar da tafi tasu, tabbas idan ba kawar da Dr Yoohan sukaiba a duniya rayukansu da hanyar cin abinsu na a cikin garari.       (Ni dai nace Humm).       Shi Yoohan baima saurari amsawar Dr Sa'ad ɗinba, dan tuni yayi wurgi da wayar saman gado cike da takaicin likitoci irin Dr Sa'ad, da a kullum basu da kishin ƙasarsu da jama'arsu, burinsu sudai kuɗi kawai da taƙama da aikinsu. Da hanzarinsa ya fito ainhin Office ɗin yana faɗin, “Rich Please ka bincika min idan akwai jirgi mai tafiya kano daga nan zuwa mintuna talatin”.        Da sauri Richard ya fita daga office ɗin zuwa nasa, dan yabar wayarsa a canne. Shi kuma Dr Yoohan yaja Laptop ɗinsa dake saman tebirin daga tsaye ya shiga dannata da sauri sauri cikin ƙwarewa. A haka Solomon ya shigo ya samesa, batare daya tsayaba yay saurin shigewa bedroom ɗin domin fidda masa kayan da zai saka dan Richard ya sanar masa halin da ake ciki, kuma shi Dr Sa'ad ya fara samu a waya kafin Richard ma.          Dr Yoohan na kammala tura abinda zai aikama Dr Sa'ad ya nufi ɗakin shima. bai wani damu da tsayawa duba kayan da Solomon ya ajiye masanba ya ɗauka ya fara ƙoƙarin sakawa, shi kuma Solomon ya fito ya bashi waje.         Shirin yake ransa duk a jagule da takaici, yana kammalawa ya fito jacket ɗin suit ɗinsa a hannu, necktie ɗinma haka. Gashinsa kansa yau sama-sama ya samu gyara. Haka yake shi, a kullum matsalar al'umma itace tashin hankalinsa da damuwarsa. Da kaga damuwa a idanunsa to patient ɗinsa na cikin matsala ne. Baiko kalli inda Solomon ke tsaye da jikkarsa a hannuba ya nufi hanyar fita fuskarnan babu alamar wasa.       Kusan cin karo sukai da Richard dake ƙoƙarin shigowa ya sanar masa an samu jirgi, kuma cikin amincin ALLAH zai tashi nan da mintuna goma sha bakwai ne, da ƙyar akama samu ticket ɗin guda biyu. A yanda Dr Yoohan yasan garin Lagos da yammaci irin haka yasan kafin su isa airport ma lokacin tashin jirgin ma ya wuce, dan haka ya yanke shawarar su tafi a Ambulance kawai zasufi samun hanya da sauri.        Rich kansa yayi na'am da wannan tunanin na Yoohan, dan haka yama yanke shawarar kaisu da kansa ko Yoohan ɗin zai kuma samun nutsuwa.............✍ _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻. [4/7, 10:56 AM] Amina Mama: _ANNUR PERFUMES: GIDAN KAMSHI KENAN.! WANI KAYA SAI AMALE! HAKAN TAKE, INA MASU NEMAN INDA ZASU SAMU INGATATTUN KAYAN TURARE NA GIDA DANA JIKI DANA KAYA NA MAIDUGURI? KU MATSO KUJI! NESA TAZO KUSA, ANNUR PERFUMES. KAMFANIN TURAREN MAIDUGURI NE DA RESHEN SA KENAN JIHAR KANO. MUNA DA KOWANE IRIN SAMFURIN KAYAN KAMSHI KAMAR SU; TURAREN WUTA NA KAYA DANA JIKI DANA TSUGUNNO, MUNA DA KHUMRAH, KULACCAM GANGARIYA DA ALMISKI(THAHARA/AYSHA/BAKI DA JA) MUNA DA DECORATIONS NA TSINTSIYA DA SAURAN SU, AKWAI KAYAN MATA INGATATTU MAI SA KISHIYA KWAFA, BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA, MUNADA KAYAN MATSI YAN GASKE, NAMU BA IRIN NASU BANE. _ _DUKA WADANNAN JERIN TURARUKA MUNA BADA SU AKAN FARASHIN SARI KO SAYI ‘DAI DAI. ADIRESHEN MU; MUNA KANO, UNGUWAR GAIDA, LAYIN MASALLACIN IMAMU MALIK. LAMBOBIN TARHON MU: 07086341096/07069036534. MUNA AIKA KAYAN MU KO’INA A FADIN NAJERIYA, KAMSHI RAHAMA NE YAN’UWA, MUSANMAN KAMSHIN ANNUR PERFUMES DAKE SANYA NUTSUWA DA KWANCIYAR HANKALI. GA ARHA GA LAGWADAR KAMSHI SAI ANNUR PERFUMES_ ____________________________ 13 .................An gudanar da gagarumar walimar aure da saukar alkur'anin marayun ALLAH da waɗanda son zuciya ta saka iyayen nasu ajiyesu saboda gudun abin kunya. Sai kuma UBANGIJI mai rahama yay musu gata ta hanyar waɗanda basusanma sanda kikaje kika aikata ɓarnanrba.      An sha wa'azi mai ratsa jiki ga manyan malamai, tare da addu'oi ga waɗan nan yara. Sai ƙyaututtuka daga manyan mutane ta hanyoyi da dama. Al'amarin dai sai muce Alhmdllh. Sosai su baba malam da ƙannensa da Hajjo harma da iyalansu suke cikin dunbin farinci da zagayowar wannan rana a garesu, dan kuwa ba itace ta farko ba, dan wannan shine karo na bakwai da zasu aurar da yara a cikin wannan gida. Al'amarin kam ya burge mutane matuƙa, inda wasu sukaji inama sune da wannan ƙyaƙyƙyawar zuciyar haka irin tasu baba malam. Yayinda wasu kuma suka ɗauki ɗammarar shigowa cikin tawagar a dama dasu da iya abinda ALLAH ya hore musu suma. Komai ya ƙaytar, dan ya tafi cikin nutsuwa, sarki ya bama waɗanan yara ƙyaututtuka, hakama Gwamna daya turo wakilinsa dan shi bai samu damar zuwaba ya dai bada tashi ƙyautar ga waɗannan angwaye da amare.           Su Nu'aymah ansha kaikawo, dan kuwa sunyi tiɓis kamar sune amarorin. Bayan an tashi daga walimar da ƙyar suka rarrafa masaukinsu suna maida numfashin wahala. Su dai su Umm sunbi mazansu sun koma gida kamar yanda sukazo tare. Su Nu'aymah d Hajjo kuwa suna nan sai sunga ƙwal uwar daka. ________________________              Bayan sallar isha'i baba malam ya tattara ƴan uwansa su duka uku a falonsa. A tare sukaci abincin dare, tare da tattauna yanda walima ta tafi cikin aminci da farin ciki babu wata matsala. Sunyi godiya ga UBANGIJI da ya zamemusu garkuwa, sannan baba malam dake tsaye akan komai.      Ɗan murmushi kawai yayi batare da yace dasu komai akan hakanba. Kafin cikin nutsuwa ya nuna musu leda ruwan ƙasa da aka kawo ɗazun kafin walima tare da kayan abinci. Kasancewar bai samu zama dasu ba ɗazun sai bai sanar dasu komaiba ya bari sai sun dawo gida suyi maganar a tsanake sannan su duba abinda ke a ciki.      Abba Musbahu da ya kasance ƙarami shi baba malam ya mikama ledan yana faɗin, “Musbahu buɗe muga minene a ciki, dan shi manager ɗin kamfanin da aka kawo kayan ta hanyarsu yace dukkan bayanan da muke bukata zamu samu anan. Amma mu kwantar da hankalinmu wanda ya bada ɗin baiyi da wata manufa ba, kuma shi yayine badan musan wanene shi ba, idanma muna tsoron wani abune to duk abinda mukaga be kwanta mana a raiba ko wata matsala ta biyo baya to mu nemesa shi, zai kaimu ga mai saƙon idan buƙatar hakan ta taso”.       A tare sukace masha ALLAH, ALLAH ya sakanka masa da alkairi, ya biyasa da sakamakon abinda yafi wanda yayi. Shima ALLAH ya faranta masa fiye da yanda ya farantama mabukata.       “Amin". baba malam ya amsa musu, yayinda Abba Musbahu ya fiddo abinda ke naɗe cikin leda mai ƙyalƙyali. Buɗe ledar yayi sai ga madaidaicin kwali ya bayyana. ya buɗe kwalin shima. Sun sami envelope guda biyu, ta farko check na kuɗi da suka basu mamaki fiye da zato. Dan a irin wannan halin da ake ciki mai bada ƙyautar irin waɗanan kuɗi masu yawa haka ai dole a jinjina masa. Sai zungureriyar wasiƙa, wadda bayanan cikinta ke magana akan su bada sunan yara talatin na gidan marayun da suka ƙare sakandire, ya ɗauki nauyin karatunsu na jami'a harsu ƙare, maza 15, mata 15. sai sunan kuma wasu ashirin din, maza 10 mata 10 sukuma waɗanda suka kare karatun zai nema musu aiki. Daga ƙarshe yace yana roƙonsu alfarmar sakashi cikin jerin mutane da zasu dinga hidima ga wannan gidan marayu gwargwadon ƙarfinsa.          dukansu ajiyar zuciya suka shiga saukewa na mamaki da al'ajabin wannan mai saƙo. Kafin su shiga ja masa dogayen addu'oi, daga ƙarshe suka tattauna sosai akan lamarin. Sun yake shawarar faɗama UBANGIJI akan lamarin. Idan alkairine kuma mai wannan ƙudiri bada niyyar cuta musu ya zoba ALLAH yay riƙo da hannayensu gaba ɗaya. Idan kuma da wata manufa tattare da shi ALLAH yay musu maganinsa tunkan ya samu damar shiga jikinsu balle ya cutar da bayin ALLAH.      Daga haka suka tashi akan zasu mikama UBANGIJI kukansu tsahon kwanaki uku, inda zuciyarsu ta karkata akan al'amarin zasu ɗaukesa a matsayin shine zaɓin da ALLAH yay musu, saisu yanke hukunci akan hakan. zasu cire kuɗaɗen daya rubuta ɗin a maidasu asusun gidan marayun.  bayan an gama ƙurar ɗaurin auren gobe idan ALLAH ya kaimu kuma saisu tantance yaran daya buƙata game da cigaban karatunsu da kuma waɗanda za'a nemarwa aiki. *_ABUJA_*                Bayan tafiyar Yoohan da kamar awa biyu sai ga papa da tawagarsa shi kuma ya dawo gida. Dama sunje taron manyan fastocine daya gudana a jihar Lagos, yau kwanansu biyar kenan a can. Ya samu tarba daga iyalansa da ma'aikatan gidansa, inda madam Chioma ke maƙale da shi har sashensa tai masa rakkiya.        Bayan ya ƙimtsa ya fito sukai zaman yin lunch su duka a dining, sosai suka cika falon da surutu kamar ba abinci suke ciba, kowa na bama papa labarin abinda ya faru da baya gida. A cikin surutun nasu ne Abraham ke faɗama papansu an fasama Brother Yoohan motarsa a kano.      Cak Papa ya tsaya daga cin abincin yana kallon Abraham ɗin, kafin ya maida kallonsa ga Madam Chioma da a lokaci guda ɓacin rai ya mamaye fuskarta. “Mi naji Abraham na faɗa Darling?”. Kanta ta jinjina masa tana ɗan karta cokalin hannunta akan filet ɗin abincinta, “Hakane Honey, jiya da yaje Kano abin ya faru, dama jira nake ka dawo asan matakin daya dace a ɗauka, shiyyasa bance masa komaiba dan karya ce bayaso ayi komai dan kasan halinsa dai”.       Ɗan dukan table ɗin papa yayi da ture kofin da aka zuba masa lemo ya faɗi. A tare yaran duk suka zabura dan tsorota. Ya miƙe a fusace yana faɗin, “Miyasa tun a jiyan baki sanar minba, Gebrail ka tattaramin guards ɗin Yoohan gaba ɗayansu yanzun nan”.             Cike da jin daɗi Gebrail ya amsa ma papa yana miƙewa. Dan shima burinsa a ɗauki matakin dama.       Cikin mintuna ƙalilan guards ɗin Yoohan suka taru a falon, kallo guda zakai musu ka fahimci hankalinsu a matuƙar tashe yake. Musamman da suka shigo falon suka iske Papa nata kai kawo rai ɓace, kai kace gadin wani abu ya keyi. Sunkai tsayuwar mintuna goma kansu a ƙasa kafin ya kallesu da jajayen idanunsa.          “Inaga baku da wani amfani game da tsare lafiyar Yoohan, zamu sallameku mu canzaku da waɗanda zasu iya, dan na inhar kune zaku cigaba da kulamin da yaro wataran sai an masa yankan rago kuna kallo baku iya yin komaiba akai”.      Cikin ƙololuwar tashin hankali suke bashi haƙuri da roƙonsa. Suka ɗora da faɗin, ba laifinsu bane suma, boss ɗin nasune ya hanasu kowanne irin yunƙuri akan yarinyar. Kuma suna isowa sukaima Madam bayanin komai da ya faru....       Tsawa papa ya daka musu wadda ta sakasu yin shiru lokaci guda. “Idan ya hanaku ɗaukar mataki miyasa bazaku kirani tun a lokacin ku sanar mini ba?! Tunkan ku fara aiki ban sanar muku duk randa kukayi kuskure wani abu ya faru da yarona abakin aikinku ba?”.         Ka faɗa mana sir. Suka bashi amsa kowanne rai a dagule a tsorace kuma.      Hannu yasa ya bugi kujerar gabansa, “Oh shine kuma baku tuna wannan dokarba?!!”.          Madam Chioma dake bayansa ta kama hannunsa ta riƙe cikin nata tana ɗan murzawa alamar lallashi, dan bata buƙatar a sallami guards ɗin, itama suna mata nata aikin ne daban. “Darling relax, kasan halin Yoohan ɗin namu ai, kai musu afuwa su kiyaye gaba kawai. Sai kuma musan abinda ya dace a ayi, idan aikawa za'ayi a kamo mana yarinyar shikenan, dan bana goyon bayan a barta”.         Iska ya furzar daga bakinsa, ya zare hannunsa daga nata ya zagaya cikin falon sosai ya zauna a kujera. Kwalba dake a saman ƙaramin tray ya ɗauka ya tsiyaya abinda ke a cikinta a kofin glass ɗan ƙarami da shima yake a kan tray ɗin. Gaba ɗaya ya juye a baki yana ya mutsa fuska, kafin ya ajiye kofin ya kallesu ɗaya bayan ɗaya.         “A ina abin ya faru?”. “A ƙofar gate ɗin wani orphanage ne sir, kuma muna ƙyautata zaton yarinyar itama ƴar gidan ce, dan ciki boss yasa muka shiga akai treatment ɗin yaron”.         “Daga nan zuwa safiyar gobe ku tabbatar wannan yarinyar tana nan cikin abuja, inba hakaba a bakin aikinku”.         A tare suka saki murmushin jin daɗi, dan koba komai suma dama ƙulle suke da yarinyar, da kuma takaicin hanasu ɗaukar mataki da Yoohan yayi jiya. Yanzukan sun sami damar cin ubanta dai-dai gwargwado. Cike da girmamawa da alƙawarin yin abinda papan ya sakasu suka amsa. kafin ya basu izinin barin falon.       Ko cikakken mintuna ashirin basu ƙaraba a gidan suka ɗakko hanyar kano duk da kuwa a lokacin ƙarfe ɗaya na rana ya gota.       Tofa, ana wata ga wata kenan😳😳 . _____________________ *_NU'AYMAH_*             A ɓangaren su Nu'aymah suma a washe garin wannan ranar bayan sakkowa sallar juma'a a massallacin aka ɗaura auren yara talatin da shida dake a gidan marayu na ƊAN JIBIYA FAMILY. Inda bayan kammala ɗaurin auren aka rakasu da addu'oin fatan alkairi kuma.          Da yamma su Nu'aymah suka ɗanyi shagalinsu iya mata a sashen matan, suma mazan anguna sukayi nasu a sashensu tare da sauran angunan da ba'a gidan marayun suke ba suma. Bayan sallar la'asar kusan ƙarfe biyar da tai dai-dai da isowar tawagar guards ɗin Yoohan gidan marayun aka kwashi amare gaba ɗayansu aka miƙasu ɗakunan mazansu, bisa rakkiyar iyayensu su baba malam. bayan doguwar nasiha da sukasha daga garesu tamkar yanda mahaifa kema ƴaƴansu idan zasu miƙasu gidan miji.         Duk wani jan ido da barazanar Guards ɗin Yoohan securitys sun hanasu shiga cikin Orphanage ɗin, acewarsu sai dai su faɗi miya kawosu anan gate, idan sunga da damar barinsu su shiga shikenan, idan sunga babu damar hakan kuma sai dai su juya. Ran guards ɗin ya ɓaci matuƙa, sunji kamar su harbesu kowama ya huta. amma sai suka danne sukai musu bayani akan abinda ya kawosu, tare da tabbatar musu suna tare da ƴan sanda.       Duk da securitys ɗin gidan marayun sun gane wa ake nufi da kuma miya faru jiya sai suka nuna bama su ganesuba, dan a ganinsu bai kamata su bada damar da za'aci zarafin ƴa ɗaya tilo ga wanda bai taɓa gajiyawa wajen musu hidimaba. Sun kaɗasu dambu taliya sunce basu gane Nu'aymah ba, su bama susan anyi wani abuba.      Ran guards ɗin yayi ƙololuwar ɓaci, sai dai ɗaukar mataki ya gagaresu, dan suma securitys ɗin gidan marayun bawai kanwar lasa bane. Sun san taɓasu babban bala'ine ga ogan nasu papa balle su ɗin karan kaɗa miya. Dan haka suka bar orphanage ɗin ransu a ɓace, akan zasuje su sake shiri gobe su dawo.      Hotel suka kama, kafin su kira papa su sanar masa da komai daya faru. ★★★★          Su Nu'aymah da basusan wainar da ake toyawaba ana kammala miƙa amare baba malam yasa Yah Ahmad ya tattara masa su aka wuce dasu gida badan sunso hakanba. Dan so sukai sukam sai sunyi sati ɗai-ɗai a gidan kafin su koma gida. Sai dai baba malam ya ɓata musu shirinsu.      Aiko koda suka koma gidan sai suka dinga fushi da kumbure-kumbure. Kayan biki da baba habi ta haɗa musu ma sunƙi kulawa. Babu wanda yabi takansu a gidan, saisu Kubrah ne ma ke musu dariyar tsokana suna sake ƙulal dasu dan duk suna sashen Hajjo ne da suka dawo tare. ____________________               Gaba ɗaya ran guards ɗin Yoohan a ɓace yake, tunda suka iso hotel ɗin da suka kama basu zaunaba, sai faman ƙulle-ƙullen yanda zasu sami Nu'aymah da matakin da zasu ɗauka a kanta sukeyi. Kai kace wata babbar ƴar ta'adda suke bibiya.       Sun ƙulla yafi sau hamsin suna warwarewa. Suna tsaka da sake ƙullawa saƙo ya iso garesu daga hannun ɗaya daga ma'aikatan hotel ɗin. Number wayace daga wani, ya basu damar su kirashi idan suna buƙatar sanin inda wadda suke nema take..               Da yake burinsu kenan jiki na ɓari suka kira kuwa. Ba'a ɗagaba har sai da ta kusan tsinkewa. Ƙinyin magana akayi. sai da ɗaya daga cikin guards ɗin ya fara magana.       “Duk da bamusan ko wanene ba, mun maka alƙawarin inhar ka sanar mana inda yarinyar take zamu biyaka da kuɗi masu nauyi, oganmu ma zai maka ƙyauta ta musamman”.        Batare da an basu amsaba aka yanke wayar. Kallon juna suka shigayi tambayoyi fal ransu. Kafin ɗayansu ya iya furta wani abu sai ga saƙo ya shigo. Da sauri suka buɗe ganin Number da suka kira ɗince. Ba komai bane a saƙon face cikakken address ɗin gidansu Nu'aymah, da sunanta harma da hotonta.     Daɗine yay mugun kamasu, dan kuwa sun sake tabbatar da itaɗince, dan haka jiki na rawa suka sake kiran wanda ya tura musu ɗin. Yanzun ma dai baiyi maganaba, sai sune suka buƙaci ya turo musu accaunt details nashi ko nata zasu tura masa ladan aikinsa. Ƙitt aka yanke wayar batare da ance komaiba. Mintuna kaɗan kuwa saiga accaunt Number an turo. A take suma sukaima papa massege bayan sun kirashi sun sanar masa komai.                   Har a lokacin cike yake da ɓacin ran abinda ya faru, dan yaje yaga yanda akaima motar bugu na fitar hankali, shiyyasa ransa ya sake ɓaci, ya kuma tabbatarma kansa ko ɗiyar uban wacece yarinyar sai ta yabama aya zaƙinta.            Babu ko tantama ana turo masa accaunt details ɗin ya antayama maishi kuɗi masu tsoka, dan a ganinsa bukatarsa ta biya. Mizaisa yaji ciwon biyan wanda ya taimakesu. ________________________________ *_NU'AYMAH_*                Yau sama-sama Nu'aymah ta wayi gari, dan ta tashi da ciwon ƙafa alamar zuwan period ɗinta. Ita dama takan fara da ciwon ƙafane, randa yazo kuma zataita amai har saita jigata. Kafin daga bisani ta koma normal sai shegen ƙwaɗayi kamar taci mutum ɗanye.       Tunda Umm ta shiga tadasu sallar asuba ta lura batajin daɗi, dan maimakon kwance saita isketa zaune ƙasa a bakin gado kan kafet ta kife kanta a kan gadon. Yusrah da Amal nata barcinsu a kan gadon su. Ita ta fara tadawa kafin su Amal, har zata juya ta fita sai kuma ta dakata ta kalli Nu'aymahn data maida kanta ta kife tsakanin ƙafafunta.......       “Ke kuma lafiya?”. Da ƙyar Nu'aymah ta ɗaga kai ta kalli Umm, sai dai gudun kar ace ta shirya aje asibiti a mata allura sai ta daure tace, “Umm lafiya lau, kawai gajiyace tasa ƙafafuna ciwo”.       Ɗan ƙura mata idanu Umm tayi na wasu mintuna, kafin ta janye tai ficewarta batare data sake cewa komaiba. Yusrah ce ta ƙaraso wajen Nu'aymah ɗin ta durƙusa. “Baby ƙarya kikaima Umm wlhy, daga gani baki da lafiya”.     Yamutsa fuska Nu'aymah tayi kaɗan tana maida ƙwallar data cika mata ido. “Ƙafafuna ke ciwo wlhy Yusrah, nasan kuma period ɗinane zaizo zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu ko anjima”.          Amal dake fitowa daga bayi tace, “To miyasa kikaƙi faɗar gaskiya?”. Yusrah data harbo jirgin Nu'aymah tai saurin cewa, “Allura”. A tare suka kwashe da dariya ita da Amal. Nu'aymah kuma tai tsaki idonta cike da ƙwalla ta miƙe. Da ɗingishi ta shiga bayi batare data kula dariyar dasu Yusrah ke mataba har yanzun.          Bayan sun idar da salla Yusrah da Amal suka fice taya iyayensu aiki, Nu'aymah kam saita koma saman gado ta kwanta. Babu jimawa barci yay gaba da ita.      Umm da duk ta gama fahimtarta bata nemeta ba, dan tasan zata gama zagayenta ne tazo ta nemeta. Bayan sun kammala breakfast ita da ƴan aiki ta shirya na baba malam da sauran ƴan uwansa a falonsa da kanta kamar yanda ta saba inhar duk suna gari, dan tare sukecin abincin safe da dare. Na rana ne dai bai zama dole su dukansu suna a gidaba shiyyasa. Garama idan ta kama juma'a ace dan duk basa zuwa ko ina a wannan ranar sai massallaci.         Sai da taga komai ya mata yanda takeso sannan ta saka turaren wuta ta leƙa bedroom ɗinsa. Yana wanka, sai kawai ta buɗe Wadrobe ɗinsa ta zaɓo masa kayan da zai saka, saboda yau zasuje taron wani wa'azi a jihar katsina. Bayan ta ajiye masa duk abinda tasan zai buƙata ta fita zuwa ɗakin Muhammad danta taimaka masa yayi shirin makaranta shima. *_08:15am_*        Kusan takwas da kwata su baba malam suka hallara a falonsa shi da sauran ƴan uwansa domin karyawa. Sun sake gaisawa cikin girmamawa kamar yanda suka sabama kansu. Kafin su zauna su fara karyawa abin cike da birgewa.      Sunyi nisa da cin abincinsu sukaji sallama. A tare suka amsa idonsu akan ƙofar. Ƙarasawa ciki falon Abbas da yay sallamar yayi. Ya durƙusa har ƙasa ya gaidasu. kafin cikin damuwa yace, “Abba ƴan sandane ke sallama”.        “Ƴan sanda kuma Abbas? Lafiya dai ko?”. Baba malam dake kallon Abbas babu ko ƙyaftawa ya faɗa.        “Abba ban saniba wlhy, amma sun nuna wai an turosu su tafi da Nu'aymah ne”.        Ran Abban Adawiya a ɓace yace, “Wace irin Nu'aymah kuma? Miya haɗata da ƴan sanda banda shashanci irin naka Abbas?”. “Wlhy Abba haka sukace, dan hotonta ma suka nuna”. Miƙewa sukai su duka huɗun, sai dai su uku suka fara fita, kafin baba malam yabi bayansu..............✍ _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻..________________________ *ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*        *_KAJI shahararrun kuma mandiyoyin ƴan ƙwalisar kawo kayan kitchen masu tafiya dai-dai da zamani. Idan nace nadaban ina nufin suɗin nadabanne wajen kaya ƴan gaske dake ƙawata kitchen ɗin amarya harma dana uwargida ƴar ƙwalisa. Ka siya ka tabbatar ka saya ɗin ko a gaban tsaranka sai ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE. sunan kayansu sa kishiya cin bashi🤣, dan tana ƙyalla ido taga kitchen ɗinki tsarin amerikawa tuni zata fara ƙwafa da tunanin zuwa gidan delu dillaliliya mai saida kwanika. Sai dai kuma kama da wane akace bata wane, dan haka ku maza ku garzaya ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE. domin samun naku kuma. Suna kawo kaya daga ƙasashen ƙetare akan farashi mai sauƙi da rahusa. Suna order ɗin products kamarsu, dukan kayan kitchen na zamani, bedsheets, shoes dade sauransu, products ɗinsu pre-order ne dake zuwa akan lokaci batare da mai kaya ya ƙosa da jira ba ko samun matsala. Zaku iya samunsu a Number waya kamar haka ko Location nasu. Phone number: 08102393622. Location Gombe. Amma Zasu iya turawa kowani gari dake a lungu da saƙo na ƙasarnan. Sayen nagari maida kuɗi gida. Ku garzaya kar ayi babu ku. Da ƙyar nasha yafi da ƙyar aka kamani inji masu iya magana😉😘😘😍😋._* _______________________________ 15 .................Kaɗan ya rage su makara a hanyar zuwa airport, ALLAH dai ya taimakesu suka isa gab. Sai da Richard ya ga tashin jirgin sannan ya bar Airport ɗin yana mai kiran Dr Sa'ad ya sanar masa ga Dr Yoohan nan ya taho su kwantar da hankalinsu.       Duk da Dr Sa'ad baiso hakanba sai ya amsa masa harda addu'ar isowarsu lafiya. A ƙasan ransa kam ji yake kamar zuciyarsa zata babbake da wuta dan takaici da tsanar Dr Yoohan ɗin da bai taɓa tare masa komai a duniyaba bayan nusar dashi ya san kansa kawai.      Yana sauke wayar daga kunnensa kiran Madam Chioma na shigowa. Ɗagawa yay da hanzarinsa, dan yasan dai bai wuce ta kira Number Yoohan ɗin bata shigaba ko bai ɗagaba. Ya gaidata cikin girmamawa kamar yanda ya saba, kafin ya ɗora da faɗin, “Mom lafiya dai ko?”. Daga can tace, “Eh Richard, lafiya, amma na kira abokinka sau uku bai ɗagaba, nayi zaton ko yana akan aikine idan ya kammala zai kirani, sai dai har yanzu banga kiransaba. Na kuma nemesa yanzu da kaina wayarsa bai tafiya. Shine nace ko lafiya?”.        Murmushi yay yana ƙara jinjina ƙaunar wannan uwa da ɗa a zuciyarsa. Cike da kulawa yay mata bayani yanda zata fahimta, sai dai yanda tai azamar katsesa jin ya ambaci kano sai abin ya nema firgitashi. Kafin ya samu damar tambayarta dalili harta yanke kiran. *_ABUJA_*        Hankalin Madam Chioma a tashe tai kiran Guards ɗin Yoohan dake shirin tahowa da Nu'aymah Abuja. Cikin azalzala ta sanar musu karsu taho su ajiye Nu'aymah a police station ɗin maza su nufi airport su tarbi Yoohan gashi nan ya taho da ga Lagos. Tai mugun basu gargaɗi akan inhar wani abu mara ƙyau suka bari ya faru da Yoohan ɗin yau to su tabbatar a bakin aikinsu kenan, bayan horo mai tsanani da zasu fuskanta kuma.               Sanin Madam Chioma zata aikata fiye da abinda ta faɗa inhar akan Yoohan ne ya saka guards ɗin Yoohan bin dukkan umarninta. Har an fito da Nu'aymah da ko harara babu wanda yay mata a station ɗin, hasalima tana a office ɗin d.p.o tunda aka kawota suka sanarma d.p.o halin da ake ciki game da umarnin mahaifiyar uban gidansu.        Babu musu ya amince da ajiye Nu'aymah har suje su dawo, su kuma suka shiga motocinsu suka bar station ɗin zuwa airport ɗakko Dr Yoohan da suka san nanda mintuna ƙalilan ne jirginsu zai sauka.       Murmushi Nu'aymah tayi tana mai buɗe tafin hannunta ta kalli ƴar takardar da baba malam ya saka mata lokacin daya kamo hannunta. Takardar ta sake buɗewa ta karanta addu'ar dake ciki tana murmushi, wata irin ƙaunar mahaifinta da tausayinsa na ratsata a zuciya da ɓargo. A yau ta ƙarajin ƙwarin gwiwa akan shirin mahaifin nata. Wanda daga ita sai shi sai ALLAH daya hallicesu sukasan da shirin. Amma ko Umm yaja mata gargaɗi mai ƙarfi akan karta bari ta sani, bakomai yasashi yin hakanba sai wani dalilinsa da itama yace ba yanzu zai sanar mataba sai nan gaba.  ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 ______________________★             Gaba ɗaya Yoohan ji yake kamarma jirgin baya wani sauri, duk bayan mintuna sai ya kalli agogon hannunsa yayi ƙaramin tsaki da Solomon ne kawai ke jinsa, yay masifar ƙosawa yaga sun sauka. A yanda hankalinsa ke a tashe har sai da Solomon yaji tausayinsa ya kamasa. Yana mamakin yanda Dr Yoohan sam babu wani ƙyashi ko ƙabilanci a ransa, game da aikinsa bai taɓa banbanta kai ɗan wane addini bane ko kai ɗan wane yankine. Kansa tsaye yake ƙoƙarin sa, shiyyasa a kullum ALLAH ke sake ɗaukaka darajarsa, dan kullum bayin ALLAH cikin masa addu'oi suke a zahiri da baɗinin zuciya.           Duk da burinsa nason jirgin yay saurin sauka ahakan bai hanashi fita cikin nutsuwa ba lokacin da jirgin ya taɓa ƙasa. Yanda yake tafiya kawai ya isa abin kallo ga mutane. Duk da fuskarsa kullum a cinkushe take hakan bai hana ya ɗauki hankalin masu kallonsa daga maza har mata ba.          “Welcome sir”. Yaji an faɗa Lokacin da suke isowa wajen masu taxi shi da Solomon dake a bayansa. Kamar zai share sai kuma dai ya juya. A bazata idanunsa suka sauka akan guards ɗinsa waɗanda baiyi zato ko tsammanin ganiba.      Da sauri suka ƙaraso gabansa zuciyarsu na dukan ɗari-ɗari ganin kallon da yake musu na tsagwaron mamaki da tuhuma, cike da girmamawa suka shiga gaishesa ɗaya bayan ɗaya, kafin su ɗora da masa bayanin Mom ce tace suzo su tarbesa.       Duk da akwai magana a bakinsa game da ganin nasu a kano sai ya share bai yiba. Ya nufi inda ɗaya daga cikinsu ya buɗe masa mota ya shiga.        Sai da suka fito da ga airport ɗin gaba ɗaya suka hau kan titi sannan ya jefama driver da Solomon ke kusa da shi tambaya a bazata.      Cikin harshen nasara yace, “Miya kawoku kano?”. Cikin faɗuwar gaba driver ya kallesa ta madubi. Sam bama kallonsu yake ba, hankalinsa nakan waya yana dannawa. Cikin ɗan rawan baki na rashin gaskiya driver ya bashi amsa da faɗin, “Sir M... Madam ce ta aikomu”. “Yin me?”.Yoohan ya faɗa da ɗago fararen idanunsa ya zubama drivern cike da nazari. Sosai kallon ya firgitashi, dan anyi sa'a lokacin da Yoohan ɗin ya ɗago idanu yayi dai-dai da ɗagowar driver shima ya kallesa.      Saurin riƙe sitiyarin yayi jin zai ƙwace masa, dan har motar sai da tayi ɗan tangaɗi kaɗan. “I am sorry sir” driver ya faɗa da sauri ƙirjinsa na dukan tara-tara ganin yana neman zubar dasu a ƙasa. Shiru Yoohan bai tanka ba, hasalima ya ɗauke kansa tamkar baiga wani abu daya faru ba. Sai ma ya ɗauka waya yay kiran Dr Sa'ad da kai hannu saman kunnensa ya gyara Bluetooth ɗinsa na fama dake a maƙale.        Solomon da duk ya fahinci akwai wani abu dangane da zuwan ƴan uwanasa kanon ya haɗiye yawu da ƙyar shima yana satar kallon madubin, ganin hankalin Yoohan ɗin baya garesu sai yay saurin maidawa ga drivern. Ƙyaftama juna idanu sukai, alamar dai sun saba da yaran. Solomon ya ɗan gyaɗa kansa yana gyara zama.      A haka suka isa asibitin batare da kowa ya sake magana ba. Tun kafin a buɗe masa shi harma ya buɗe ya fice abinsa. Da yake yau zuwan bazatane Dr Sa'ad kawai ya san zaizo sai Dr Aysha, sauran Doctors ɗin basu fito sun tarbesa ba kamar yanda suka saba.     Sai dai tun shigowar motocinsa wasu daga ma'aikatan asibitin suka fahimci shine. Yayin da gefe guda kuma da ya zama abin kallo ga mutane. Musamman ma yanda yake tafiya Guards ɗinsa na take masa baya. Waɗanda suka sanshi nata faɗin, “Dr Yoohan yay zuwan bazata, yaukam za'asha masifa musamman akan ma'aikatan dakeda sakaci akan aikinsu.      Duk da ya fahimci yanda wasu a cikin ma'aikatan ke ta guje-gujen sanarma iyayen gidansu zuwansa basuko ishesa kalloba. dan abinda ya kawosa shine kawai a gabansa ba su da shirmensu ba.      Tunda su Solomon sukaga shigewarsa sai yaja hannun ɗaya daga cikin Guards ɗin suka fito, sauran kuwa na tsaye ƙiƙam tamkar an dasasu gadin duniya🙄😏, sai zazzare idanu suke sun hana masu kai kawo ta wajen sukuni. Ba marasa lafiya da ƴan uwansu kawaiba, hatta ma'aikatan asibitin a takure suke. Masu sanya da aikinsu duka sun dage saboda jin zuwan Dr Yoohan. (ALLAH ya ƙyauta. Bazakaji tsoron UBANGIJIN daya halicceka ya baka amanar wannan aikin a ranka ba sai wani shasha mutum irinka, ba kuma komai ke kawo tsoronsa ba sai gudun karka rasa aikinka🤦🏻, ya salam. Musulmai ina muka ajiye gaskiyar tamu? Ina muka ajiye koyarwar addinin namu? Ina muka ajiye tausayi dajin ƙan da aka san mumini da shi?. Ku dubafa Dr Yoohan ba musulmi bane, baɗan yankinku bane, ba yarenku bane? Amma yana nuna fushinsa akan sakaci da cigabanku, yana nuna damuwarsa akan ƴan uwanku, yarenku addininku, yayinda ku son zuciya da burin tara duniya ya rufe jinku da ganinku. Kaje asibiti kaga ana wulaƙanta marasa ƙarfi dan kawai sunzo neman lafiya. Babban abin takaicinma yafi yawa a ɓangaren mata masu haihuwa. Kaga ma'aikatan asibiti nacin zarafinsu dan kawai sun kasance ƙauyawa ko talakawa. Haba ƴan uwana, wannan aikinfa da kike cin zarafin wasu dashi tamkar mabuɗine na gida guda biyu. Wuta ko aljannah, ya rage naki/nak ka zaɓama kanka wanda kafi buƙata. ALLAH ya shiryar damu dai, ya rabbi kai riƙo da hannun ma'aikatanmu masu ƙyawawan zukata domin rahamarka da alfarmarka🙏🏻😭). __________________________              Tunda Addah ta isko Umm a ɗaki basu iya cema juna uffan ba. Kowa ya zabga uban tagumi ne yana saƙa mai fishshesa. Sun kwashi tsahon mintuna sha biyar a haka kafin Addah ta katse shirun nasu da faɗin, “Ni nama rasa abin faɗa wlhy akan wannan al'amari, har nawa Nu'aymah take da ƴan sanda zasuzo su tafi da ita? Mi ma to tayi musu? Sannan miyasa yaya malam zai yanke wannan hukuncin mai tauri haka?”.           “Wannan sune tambayoyin da nake taima zuciyata Addah, amma sam na gaza samo amsar ko guda a ciki. Ina ƙyautata zaton a tafiyarsu bikin nan koma miye ya faru acan ya faru, dan........”            “Haba Umm miyasa zakice haka? Naga dai su a cikin Orphanage suke? To mima zata aikata da har ace mu bamujisa ba?”.       “Addah yaran nan kafa haifesu ne amma baka haifa halinsu ba, minenema bazasu aikataba tunda basa ganin idon kowa. Ballema Nu'aymah da batajin magana sam, wuyarta dai ta samu sakewa ne kawai, shiyyasa sam banason ko gidanmu tace zataje ta kwana ko wani waje wlhy, danni bansan ina ta ɗakko wannan halin nata na tsiwa da rashin kunyaba”. Yanda Umm tai maganar cikin ɓacin rai yasa Addah saurin faɗin. “Dan ALLAH karki tsaurara harshenki akan wannan abun, mudaibi komai a sannu muji inda matsalar take. Nu'aymah har yanzu yarinyace, kuma sanin kankine duk rashin ji da tsiwar Nu'aymah batayinsa ita kaɗai sai da gudunmawar su Adawiya dama, tunda halin nasu ai duk ɗaya ne.....”        “Humm Addah kema kinsan indai gaskiya zaki faɗa Nu'aymah ta fisu kaifi, dan duk abinda zasu aikata itace jagora”. “To kowa ya zauna akan ra'ayinsa danni bawai yarda zanyi ba, inaga dai bara nakira su Yusrah muji minene ya faru?”. Umm dai batace komaiba, tanata kuma ƙoƙarin danne damuwar dake cizon ranta da kukan dake yunƙuro mata a rai. Duk da Alhmdllh zuwan Addah a gareta ya sanyaya mata fushinta bakamar sanda ta shigoba.         Sallamar Yusrah da Amal ce ta saka Umm da Addah ɗagowa suna kallonsu. Basai an faɗaba, daga gani kukama sukeyi. Hakan da Umm ta gani sai ya sake karya mata zuciya, tai ƙasa da idanunta tana karanto7 addu'ar neman sauƙi da sassauci wajen UBANGIJI.      Zama su Yusrah sukai kansu a ƙasa suna sharar ƙwalla. Addah tace, “Kuka ba shi bane mafita Amal da Yusrah, ku sanar mana mikuka sani game da hakan dan musan hanyar data dace mu kama wajen amso ƴar uwarku”.       Share hawayensu duk sukai, cikin nutsuwa sukaima su Umm bayanin abinda ya faru aranar ƙunshi, sai dai sun ɓoye cewa Nu'aymah ta fasama guards ɗin kai, sundai ce ta wulwula dutse bisa tsutsayi ya daki glass ɗin motar. Hakan da tayine kuma ya saka mutanen tsayawa amma da guduwa zasuyi.       Shiru babu wanda ya iya cewa komai tsakanin Umm da Addah, sai da kusan mintuna uku Addah ta sallamesu suka tafi.          “Umm! Inaga lokaci yayi da zamu fara aiwatar da shirinmu a gidan nan gameda waɗanan abubuwan. Na kula al'amarin ƙara zurfi yakeyi kullum”.        Murmushi Umm tayi idanunta akan Addah, ta ce, “Addah wannan ai babu saka hannun kowa a ciki, itace ta jama kanta. Ni wlhy a yanzuma naji bana sha'awar sanin wanda ke aikatawar.........”         “Me yasa?” Addah ta faɗa da mamaki.      Murmushi Umm ta sake yi har haƙoranta na bayyana, tace, “Addah to minene amfanin sanin? Babu abinda sanin zai amfanar sai fitina. Idan a gidan nan yake zai zama sanadin lalacewar zumincin da aka gina bisa haƙuri da juriya. Idan kuma a waje yake za'a jawo masa tsana daga mutane a tozarta iyalansa. Addah hakan baida wani amfani a gareni, dan wlhy bana fatan kwana da wani musulmi a cikin raina koda na kwana ɗaya ne, dan bani da tabbacin wayar gari. Koma wanene UBANGIJI ya rufa masa asiri na tsahon lokaci, ya kuma fimu sanin hikimar yin hakan. To mu haƙura kawai mu barsa da UBANGIJIN ya ishesa komai”.      Ba ƙaramin ƙurama Umm ido Addah tayiba, har sai da takai Umm ɗin ta taɓata da faɗin, “Ina kika tafi kuma?”. Murmushi Addah tayi da sauke ajiyar zuciya. Tace na tafi duniyar mamaki ne da tsarkake sunan ALLAH, Umm ki godema ALLAH ya azurtaki da ƙyaƙyƙyawar zuciya wlhy........”      “Kema ai ya azurtaki da ita Addah, dan ina koyi da wasu ƙyawawan halayene daga gareki. Hakan yasa ƙaunar da nake miki ta dabance a zuciyata wlhy, fatar bakima bazata iya kwatantawa ba, kun bani gudunmawa ke da Baba wadda har na koma ga ALLAH bazan gazaba wajen roƙa muku rahama da yardarsa”.        Hawayene ya cikama Addah ido kamar yanda ya cikama Umm itama, suka kama hannun juna suna murmushi cike da ƙaunar juna da ta ginu tun ƙuruciya..............✍ (ALLAH ya bar ƙauna Umm da Addah😅😘🤗)               _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_INA MASU NEMAN INDA ZASU SAMU INGANTATTUN:_* *_HERBALS APHRODISIAC NA GARGAJIYA BANA HADIN BATURE BA MAI SIDE EFFECT..?_* *_TO KU SAURARA KUJI, DOMIN NESA TAZO KUSA.._* *_ZEE HERBALS APHRODISIAC!_* *_ZEE HERBALS APHRODISIAC!!_* *_ZEE HERBALS APHRODISIAC!!!_* *_MUNZO MUKU DA INGATTTUN KAYAYYAKI WANDA ZASU GYARA CIKI DA WAJE_*    *_MUNADA SUPPLEMENT MASU GYARAN JIKI DANA FATA, WANDA ZASA SAKI KIYI SHEKI FATAR KI TAYI LAUSHI. TAYI LUWAI! LUWAI! TAMKAR TA JARIRAI_*     *_AKWAI SUPPLEMENT NA KAYAN MATA WANDA ZASU GYARA KI, KIJI KI TAMKAR BUDURWA, SUPPLEMENTS DINMU BASU DA SIDE EFFECT, DOMIN AN HADO SU NE DAGA INGATTATTUN ITATUWA, WATO NATURAL PRODUCTS NE ACIKI._*        *_KAI BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA, MUNA DA INGATTUN KAYAYYAKIN MATA WANDA KESA KISHIYA KWAFA, WANDA DUK INDA SARAUNIYA TAKAI KIN WUCE, WANDA ZASU TSATSO MIKI MARTABAR KI DA KIMAR KI_*. *_AKWAI INGATTATTUN MAGUNGUNA, NA CUTUTTUKAN DA SUKA SHAFI DAN ADAM DAMA JINNU.. KAI DAMA WANDA BAMU AMBATA BA.. ZEE HERBALS APHRODISIAC (MASARAUTAR INGATTATTUN MAGUNGUNA KENAN)_*      *_KYAU, ARHA, INGANCI, RAHUSA... SAI ZEE HERBALS APHRODISIAC_*    *_MANHAJOJIN MU NA SOCIAL MEDIA: KAMAR INSTAGRAM DA WHATSAPP DAMA NAMBAR TARHON MU: DOMIN SHIIGA KUGA IRIN KAYAYYAKIN MU TUNTUBE MU TA_* _INSTAGRAM LINK DIN MU:_ www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac _WHATSAPP LINK DIN MU:_ https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz _NAMBAR TARHON MU_ 08169380189 *_KARKA BARI A BAKA LABARI GWARA KA BAYAR.. KIZO A DAMA DAKE YAR UWA, KI ZAMO DAYA DAGA CIKIN KASAITATTUN MATA MASU AJI.. MUNA GARIN KATSINA, SANNAN KAYAN MU MUNA BADA SU AKAN FARASHIN SAYA ‘DAI DAI KO SARI.. MUNA TURA KAYANMU A KO’INA A FADIN NAJERIYA._* __________________________________ No. 17 .............Tsitt wajen yayi, dan kuwa kowa ya kasa koda tari dan al'ajabi wannan ƴar budurwa. Dalilai biyu suka hana kowa magana a tsakanin ƴan sandan da Guards ɗin Yoohan, sai kallon Nu'aymah da sukeyi.         Ƴan sandan ganin d.p.o ya fito da kansa yasa duk sukai tsit domin girmamawa a garesa. Guards ɗin Yoohan ɗin kuwa sanin ransa a ɓace yake da sune ya hanasu cewa komai suma duk da zukatansu zafi suke tamkar ana haɗa wuta a cikinsu. Ji suke da Yoohan ɗin zai basu wata dama akan Nu'aymah da wlhy ko buzunta bazasu bari ba saboda walmakalufatun da zasuyi mata.          Buɗe baki Nu'aymah tayi zata sake magana wanda batayi zato ko tsammanin ganiba taga ya shigo cikin station ɗin. Idanunsa a kanta suka fara sauka, kafin ya maida kan ƴan sandan da sauran mutanen da abinda Nu'aymah tayi ya sakasu tsayuwar sojan badakkare suga yanda wasan zai ƙare.        Sallama ya sake maimaitawa kafin ya bisu da sannu. D.p.o da bai amsa ko ɗaya a cikiba ya maida dubansa ga Yoohan dake jira su bashi hanya ya fice, dan ko kallon inda Nu'aymah take baiyiba balle ya nuna ya fahimci danshi takeyi ɗin. Kafin yace wani abu Barrister Atiku lauyan baba malam da shima ke kallon Nu'aymah yace, “Nu'aymah lafiya kuwa?”.        Fuska ta ɓata kamar zatai kuka, tace, “Uncle nima ƙarar wanda ya sa a kawoni nan ɗin zan shigar”. Sosai ya fiddo idanunsa waje na mamakinta, sai kuma yay saurin juyawa ya kalli ƴan sandan dake a kan kantar. “Officer idan bazaku damuba dan ALLAH inason ganin d.p.o ne, sunana Barrister Atiku Salis tofa”.        Kallon inda D.p.o ke tsaye suna magana da Yoohan sukai, kafin ɗaya a cikinsu yace, “To Barrister zaka iya faɗar mike tafe da kai sai a faɗa masa”. Ɗan murmushi Barrister Atiku yayi irin na kamilan mutane. Sai kuma ya kalli Nu'aymah da gaba ɗaya hankalinta na akan Yoohan, dan batason ya sulale ya fice bata saniba.        “Ba wani abu ya kawoniba, dama akan yarinyarnan ne” yay maganar yana nuna Nu'aymah ɗin.         Ɗaya a cikinsune yace, “Indai a kantane kakeson ganin Oga to ai an sallameta ma, ganinta da kai anan tsaye wai ta kawo ƙara ne”.       Da mamaki Barrister yake sake kallon Nu'aymah. Kafin yace wani abu d.p.o da suka gama magana da Dr Yoohan ya juyo garesu yana tambayar lafiya?. Cikin ƴan sandan wani ya sake cewa, “Oga wannan shine nake faɗa maka na gani zaune tun ɗazun a waje, harma nake sanar maka kamar ban yarda da shiba. To ashe lauya ne, yazone akan batunta”. ya ƙare maganar da nuna masa Nu'aymah da ganin Yoohan zai fita ya sakata raba hankalinta biyu. Batare da Barrister ya ankaraba tayi caraf tabar wajen tabi bayansa.               Ganin zasu tsere matane ya sakata saurin zuwa tasha gaban Yoohan da guards ɗinsa ke biye da shi fuska a murtuke da haushin kuɓutar Nu'aymah daga hannunsu.         A wani irin zafafe guards ɗin sukayo kanta kamar zasu cita ɗanya. Babu ko ɗar tattare da Nu'aymah ta zuba masu harara tana faɗin, “Dalla kukuma ku bani hanya marasa lokacin kansu, ba daku nakeyiba da oganku zanyi dan shine dai-dai da ni ba marasa aikiyi irinku ba”. Ta ƙare maganar da musu alamar su matsa a kanta da hannu tana wani tsume fuska da cije baki.         Lokaci guda duk suka sake kumbura da haushinta, sai dai kallon da Yoohan ɗin yay musu ya hanasu kowanne irin motsi suka zuba mata ido cike da tsagwaron takaici da tsana..          Yoohan dake ƙare mata kallo ta cikin google ɗinsa ya wani juya idanun tare da lumshesu a lokaci guda, so yake kawai yaga iya gudun ruwanta yau dai.          Fahimtar da Nu'aymah tai bayajin hausa a karon farko tai masa magana da turanci. “Ɗan dambe ban gama da kaiba ai, dan kaima na kawo ƙararka kuma na rantse har kotu sai munje”.            Koda wasa Dr Yoohan bai tunanin jin turanci a bakin Nu'aymah ba, turancinma mai ƙyau irin haka. Amma sai ya fiske a zahiri ya shanye mamakinsa a rai, ya koma mamakin tsaurin ido da rashin tsoron yarinyar.........           Tsawa Solomon da yazo wuya ya sake daka mata yana nufosu a fusace da nufin yima Nu'aymah dukan mutuwa kozata dawo hankalinta, inma oga zai kashesane ya kashesa ɗin. Jikinsa har wani irin rawa yake.       Saurin ɗaga masa hannu Yoohan ɗin yayi alamar ya dakata. Nu'aymah dake cike da haushin rashin yin maganar Yoohan ta kalli Solomon ɗin sheƙeƙe tana nunasa da yatsa, “Kai wlhy idan baka shiga hankalinka ba saika koma garinku da tsagen yarabawan farkon ƙarni, dan wlhy agaban d.p.o ɗin can zansa a maka tsatstsargiya a kumatu tunda taurin kaine da kai mtsooww”....          Duk yanda Barrister dake a bayansu yaso daurewa da lamarin yarinyar ya kasa daurewa, da ƙyar ya iya danne dariyarsa. Shi ba komaine ya burgesa da itaba sai yanda take masifarma cikin nutsuwa, babu wani rawan kai tattare da ita da zaisa kaimata fassarar bata da tarbiyya. Tsiwarce kawai a bakinta irin ta yaran nan ƴan gata da wahalar duniyarma basusan taba sai abinda baza'a rasaba. Yana mamakin yanda ta iya tsiwa, musamman idan yay dubi da irin gidan data fito. Dan shi kansa shaidane su baba malam tsaye suke a kan ƴaƴansu fiye da tunani, sannan ada da gaisuwa kawai ke haɗashi da Nu'aymah bai taɓa kawowa a ransa tana magana mai tsayibama balle akai ga wannan tsiwar.      Gyaran murya ya ɗanyi, hakanne ya saka Nu'aymah dake zubama Solomon harara ta ɗauke idonta ta maida ga Barrister.      “Kin sanshi ne?”. ɗaya daga cikin ƴan sandan da suka biyo Barrister ɗin zasuyima Nu'aymah rakkiya gida kamar yanda Yoohan ya sharɗanta ya tambayeta yana nuna mata Barrister Atikun.           Kanta ta ɗaga masa tana harar Yoohan dake shirin barin gurin, a bazata ta tsinkayi muryarsa mai amo da nutsuwa ya furta, “Silly girl” A hankali.         Jitai kamar ya jefeta da dutse a ƙirji ko ya mata wani ƙatoton zagi, ‘ita wannan mutumin zai kira da Silly girl?’ ta yunƙura zatai magana Barrister da shima yaji abinda Yoohan ɗin ya faɗa yay saurin dakatar da ita yana danne dariyarsa. “Kinga ƙyalesa kinji, taho mutafi a maidake gida, kinga na kira Malam na sanar masa an gama komai gani zan maidake, kuma shima ya tabbatar min suna a hanyar baro katsina”. Kamar zatayi kuka ta kallesa, dan rashin barinta tai ƙarar Yoohan yafi komai tokare mata zuciya, a ranta ta raya ‘In kere na yawo zabo na yawo wataran ai za'a haɗu, indai nice wlhy kasa a ranka mun ƙulla kenan’. Da haka tabi bayan Barrister tana zubama motocin Dr Yoohan da suka bar wajen harara tamkar sunsan tanayi.      ★★★★          Koda suka iso anguwar Barrister bai ƙarasa gidanba, dan dama haka suka tsara da baba malam, to saima akai sa'a ƴan sandan sun shirya maida Nu'aymah gidan da kansu. Suna gama fakin Abban Abdallah da fitowarsu kenan daga massallaci sallar la'asar yayi kiciɓus dasu Nu'aymahr. Da mamaki ya ƙaraso ga ƴan sandan.      Yayinda suma cike da girmamawa suka nufesa. Kamar ɗazun sun gaishesa da mutuntawa. Kafin cikin nutsuwa ɗaya daga cikinsu ya fara magana. “Malam ayi haƙuri dan ALLAH a mana afuwa, munzo mu gyara kuskuren da mukayi ɗazun akan tafiya da wannan yarinya. Gata mun dawo da ita, dan bata da laifin komai ashe rashin fahimtace aka samu”.        Ajiyar zuciya Abbah su Abdallah yayi yana mai jero addu'ar godiya ga ALLAH cikin ransa, tun ɗazun da aka tafi da Nu'aymah hankalin kowa ba'a kwance yakeba a gidan, sun kira baba malam yafi sau ashirin dan su bashi haƙuri ya janye sharaɗin daya gindaya musu subi Nu'aymah amma yamaƙi ɗaga wayar. Gudun kar abin ya zafafa kuma sun kasa gayama Hajjo da tunda ta farka a barcinta wajen sha biyu take faman saka yara su kira mata Nu'aymah tai mata kitso, dan itace ke mata duk sati. Idan kuma tanajin ƴan rashin arziƙi tace bazata mataba sai ta biya. Bawai kuɗi take nufin ta bataba, furar hajjon ta ƙa'ida mai daɗin tsiya da kowa ke ƙulafuci a gidan takeso ta bata mai yawa. Dan kullum Hajjo saita zaɓi wanda ta gadama a gidan take bama furar🤣.       Sai dai duk wanda ya fita bayan wasu mintuna sai ya koma ya sanarma hajjon Nu'aymah barci take. tun bata damu ba harta fara faɗan wane irin barcine haka Nu'aymahn keyi kamar wacce bata da mafaɗi a gidan. Daga ƙarshe ta mike da nufin zuwa ta tasota da kanta bayan sallar azhar sai ga Abba Musbahu ALLAH ya kawo gidan. Shine yay mata dabarar hanata yace bara ya aika a duba kidai Nu'aymah bata jin daɗine kokuma batama gidan.      Da wannan dabarar ya wagarar da ita da hirar mahaifinsu har akai sallar la'asar, ALLAH ya taimakesu sun fito kenan da nufin shirya yanda zasubi bayan Nu'aymah koda baba malam ɗin zaiyi fushi kuma sai gata ta dawoma.        Godiya yayma ƴan sandan, ya kama hannun Nu'aymah da haushin Yoohan bai bartaba har yanzu suka shige Abba Musbahu biye da su. Su Muhammad da suka fito zasu islamiyya ne suka fara cin karo dasu, aiko cike da ihun murna suka shiga faɗin Aymah ta dawo! Aymah ta dawo!.          Hayaniyarsu ce ta fiddo ƴan gidan har Hajjo da taji abun banbaraƙau. Umm ce kawai bata fitoba dukda kuwa tanajinsu daga sashenta, ranta kuma cike yake da zumuɗin son ganin halin da ƴarta take ciki. Amma saita danne ta cigaba da azkar ɗinta na yamma.        Rungumeta iyayen mata sukaitayi, musamman ma Addah da harda ƴan ƙwallarta tana dudduba jikin Nu'aymahr. Ganin ras babu ko ƙwarzane sai yunwa da takeji da kuma fushin fuskarta saita sake rungumeta tana godema UBANGIJI daya dawo musu da ita lafiya.        Cike da mamaki Hajjo tace, “Wai mi ake ɓoyemin ne halan? Zainabun gidan ubanwa taje da har ake wannan gayar tarbar tata?”. Shiru wajen yayi kowa ya kasa bata amsa. A take takaici ya kumeta ta kwanto bakin zaninta ta fara matsar ƙwalla da juyawa zata bar wajan. Cikin sauri Abbansu Abdallah ya riƙeta yana faɗin, “Yi haƙuri Innah, bafa wani abu baneba, dama wata ƴar matsalace ta faru, to ashema Nu'aymahn bata da laifin komai an samu rashin fahimtane kawai”.        “Gidanku Lurwanu. nace kaci gidanku! Yanzu nan ni zaku maida shashasha, tun ɗazun nake cigiyar Zainabu a gidannan amma anamin yawo da hankali, ni dama naji a jikina badai lafiyaba, yarinyar da bata iya awa biyu bata shigo sashenaba indai tana a gidanan ace wuni zur banga giccintaba kuma lafiya sumul”.        “To kiyi haƙuri inna anyi kuskure, amma za'a gyara insha ALLAH”.       “Ya zanyi na haƙura, amma a faɗamin yanda akai to”.     Babu musu sukai mata bayanin komai a gaban kowa, suka kuma ɗora da bayanin ƴan sandan da suka dawo da Nu'aymah ɗin. Ajiyar zuciya kowa ya shiga saukewa a wajen da nuna jin daɗin Nu'aymah ba wani laifi tayiba. Daga haka kowa ya kama sabgar gabansa, Addah kuma ta kama hannun Nu'aymah dake yatsine fuska saboda mararta da kamar jira take ta dawo ta fara tsunkula mata.     Umm na zaune tana azkar suka shigo, dukda taji sanyin ganin Nu'aymah lafiya lau saita ɗaure fuska ta ɗauke kanta. Addah batabi takantaba ta shige da Nu'aymah toilet, ruwa mai zafi ta haɗa mata tace tai wanka ta gasa jikinta sosai. Nu'aymah dake murmushi cike dajin ƙaunar Addah ta gyaɗa mata kai.        Zama Addah tayi a bakin gado tana kallon Umm data ɗauke kai, ƙaramar dariya tai ta tsokana da son ganin Umm ɗin ta manta da komai itama tace, “Wlhy ki gama ɗaure-ɗauren fuskarki nasan ranki fes, ni wlhy yanda kike wani ture Nu'aymah har mamaki kike bani”.       Hararta Umm tai ta sake ɗauke kanta. Addah ta kwashe da dariya a karo na biyu tana faɗin, “Oho dai, duk abinda da dai zakiyi munsan mune zuciyar taki”.       Ƙin tankawa Umm tayi, dukda kuwa abinda Addah ta faɗa ɗin shine gaskiya. Tana kawaicine kawai akan nu'aymah dan kar aga rashin kunyarta akan ƴar fari, ƴar farinma wadda ta ɗauki tsahon shekaru bata samu ba. Amma kam Nu'aymah itace cikar dukkanin farin cikinta, itace kuma dukkanin hauhawar damuwarta. Shiyyasa take jigatuwa a gidan, dan inma lagontane maƙiya sun gane akan Nu'aymah shiyyasa suke jigata rayuwar yarinyar ta hanyar SARAN ƁOYE. ____________________________              *_SAUDIA_*      Ta jima tana kai kawon jiran fitowar tasa amma bai fitoba. Daga ƙarshe sai ta fahimci da alama yau bama zai fita yabar gidanba kenan. Zama tai shiru tana ƙullawa da kwancewa a cikin ranta. Ta kusan sake shafe mintuna talatin tana wannan nazari da ƴar ƙaramar ƙwaƙwalwarta da ƙuruciya ke ɗawainiya da ita. Daga ƙarshe ta miƙe bisa yarda da shawarar da zuciyarta ta ɗorata akai.       Ɗakin nasa ta nufa tai knocking, ta kusa tsayuwar mintuna biyar baiyi ko tariba daga ciki, sai da ya gama shan ƙamshinsa sannan ya bata iznin shigowa. Mamaki yay bala'in kama Adawiya ganinsa kwance a saman gado yana danne-danne a laptop, tsabar wulaƙanci ashema yana jinta ba kamar yanda tai tunanin ko wanka yakeba.       Amma sai ta danne zafin da taji bisa koyarwar Maman Aaida, da kuma son da take masa da akoda yaushe yake hanata ganin laifinsa. Gefen gadon ta zauna murya a sanyaye tace, “Sannu da aiki Yah Ab, nifa na zata koma bakajin daɗine naga yau baka fitaba”.       Sai da yaja wasu sakkani kafin yace mata “Sannunki kema” a taƙaice. Duk da hakan bai mataba saita daure bata karayaba, ta sake cewa “Yah Ab wlhy kewar Aymah nakeji dasu Amal, dan ALLAH ka bani aron wayarka na kirasu muɗan gaisa”.     Sunan Nu'aymah data sanyane ya sakashi ɗaga ido ya kalleta a karan farko, saita narke fuska harda tara ƙwalla a cikin idonta. Karan farko da tun zuwansu ta bashi tausayi, dan shiɗin shaidane bisa shaƙuwarta da Nu'aymah. Ya ɗan sauke ajiyar zuciya yana girgiza mata kai. “Ni bazaki kira kowa da wayataba”.     Hawayen da take maƙalewa suka silalo mata saman kumatu, ta haye gadon sosai kusa da shi, “Yah Ab dan ALLAH ka taimakeni, wlhy ina kewarsu musamman Nu'aymah. Ni tunda nake ban taɓa sati bama tare ba wlhy. Amma yanzu gashi har ana neman ƙulla shekara, wata takwasfa kenan ana shirin shiga na tara. Yah Ab miyasa wai kuke son rabani da itane? Kumata uziri akan laifin ta dan ALLAH, nasan tayi kuskure amma ajizancine. Yah Ab dan ALLAH kabar fushi da ita haka nan ka yafe mata”.      Kallon Adawiya yayi cikin ido, kafin ya ɗauke yana jan ƙaramin tsaki. “Ni na taɓa gaya miki fushi nake da Nu'aymah?”.       Saurin haɗiye yawu tayi jin zata saki layi, tace, “A'a baka taɓa faɗaba, to amma yanda ko maganarta bakayi, baka kiranta ai dole zan fassara haka. Yah Ab inhar zaka yafema Nu'aymah namaka alƙawarin saina sake farauto maka soyayyarka a ranta. Ko wanene shegen Ameer ɗin nan saita barsa da izinin ALLAH. Kaga tunda Yusrah bata tare ba ita saika lallaɓa su baba malam a warware aurenku a ɗaura maka da Nu'aymah. ALLAH koni da muka tare zan iya haƙura na barmata tunda dama akwai wanda nakeso”.       Duk da bai ɗago ya kalletaba maganganunta da alama sun fara tasiri a ransa. dan kuwa cak ya tsaya daga latsa lap-top ɗin yana saurarenta kawai. Kamar zaice wani abu sai kuma ya fasa ya kalleta. “Miya hanaki zuwa makaranta yau?”. ya jeho mata tambayar bisa ƙoƙarin kauda wancan zancen na farko.     Baki ta tunzura masa gaba tana matso hawaye, “Banajin daɗi, kuma kewar su Nu'aymah na damuna. Ni wlhy idanma ba tare da itaba karatunma jakanta zantayi harsai an maidani gida ko an kawota nan munyi tare”.         Karan farko a tarihin zamansu ya sakar mata murmushin da rabon data gansa tunkam a maida auransa kanta. Ya kai hannu ya lakace mata hanci yana faɗin, “A kawota nan ku hautsinamin kai da rashinjin ku”. Wani daɗine ya lulluɓe Adawiya, ta ƙyalƙyale da dariya tana gyara zama da fadin. “Wlhy Yah Ab harma ka tunamin wani abu, akwai wata tsiya da muke tafkama Hajjo ni da Aymah har yanzu bata taɓa saniba”.      Tashi yay zaune sosai ya zuba mata idanu alamar bata duka hankalinsa yana saurare. Aiko hakan ya kuma tsundumata a kogin farin ciki ta shiga bashi labarin rashinjin da sukema Hajjo dama na makaranta. Tun yana iya murmushi kawai harya ware yanata kwasar dariya. Dan rabin iya shegen nasu duk Nu'aymah ce oganniyar yinsa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya ware yana magana da bata labarin Shima abinda Nu'aymah kan masa wataran. Ya shiga buɗo mata videos kala-kala nata ita da Nu'aymah suna rashin ji batare da tasan wanene yake ɗauka yana tura masaba. Hummm ashe kan Adawiya na ja🤔🤥🚶🏻. _________________________________             Tunda suka bar police station ɗin waya yake da Rich.. Ya sanar masa cewar ya gama masa booking jirgin tafiya Kenya, hakama wanda zai biyo daga nan kano ya dawo Lagos ɗin.        Magana yayma driver da ke shirin ɗaukar hanyar Abuja akan suje airport. Duk da sunji wayar da yakeyi shi da Solomon da har yanzu haushin Nu'aymah bai barsaba shima, sai dai hakan bai musu daɗi ba. Dan sunso ace Abujar za'a koma ko hakan ya taimakesu wajen Madam Chioma da Papa da sukasan sunacan suna jiran isowarsu da Nu'aymah.          Suna isa Airport ɗin ya sallamesu akan su tafi kada suyi dare a hanya, su kuma shi da Solomon zasuyi zaman rabin awa na jiran jirgi.      Jiki a sanyaye sukai musu sallana da addu'ar a dawo lafiya suka fito daga airport ɗin. Yoohan da duk yake a galabaice da gajiya da yunwa ya ƙoƙarin kiran papa suyi magana dan baya buƙatar kuma wani abu makamancin hakan ya sake tasowa. Sannan ya lura da tsoron dake a fuskokin Guards ɗin nasa harma Solomon dake a tare da shi. Irin kuma wannan tsoron suka baro d.p.o da shi shima.      Duk da yanda papan ke masa wayar cike da ɗoki ga Yoohan ba haka bane. Sama-sama yake bashi amsar duk tambayar da yay masa wadda gaba ɗayanta akan lafiyarsace.      Sai da ya bari papan ya kammala kafin yay masa magana ta nutsuwa akan case ɗin Nu'aymah, ya kuma nuna fushinsa sosai akan matakin da papan yaso ɗauka akan ƙaramar yarinyar da ko hankali bata gama mallaka ba.          Daga can sai papan ya danne nasan haushin ɓata masa shiri da Yoohan ɗin yayi akan Nu'aymah ya koma lallashinsa dan baya ƙaunar fushin ɗan nasa kamar yanda Madam Chioma ta tsana itama. Ya jima yana lallashinsa dan har lokacin da jirginsu ya gama shirin ɗaukar masu tafiya sannan sukai sallama. Wayarce ma ta ɗauke hankalin Dr Yoohan daga uwar yunwar dake cin hanjinsa da gajiya..............✍ Ku ƙara haƙuri dani fa dai dan ALLAH 🙏🏻. _____________________ SAHFAT PREORDER! ______________________         Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗. SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya. Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske. *_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._* _To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_. Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU. Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa. *_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_* _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻._____________________ SAHFAT PREORDER! ______________________         Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗. SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya. Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske. *_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._* _To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_. Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU. Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa. *_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_* _____________________________        *_SAUDIA_*      .............Kai kawo taketa faman yi a falon nasu dake wadace da sanyin ac da ƙamshi kai kace safa da marwa take gudanarwa. Ta canja sosai, dan komai na jikinta ya ƙara girma da cika. Daman can duk tafi su Nu'aymah girman jiki kasancewar ta ɗakko jikin Addah. Yanzu kuma darajar aure saita sake bata damar buɗewa tamkar ba ƴar shekara goma sha takwas ba.     Tabbas tana samun ci da sha da sutura duk irin wadda ta buƙata, sai dai a watanni tara kenan da aurenta da Yah Abdallah babu wata rana da zata ware ta dangantata da farin cikinta. Idan har ta samu kulawarsa to na wasu awoyine da zai biya buƙatarsa. Baya son zaman gidan sam, ita kanta har mamaki take da al'ajabin ina yake zuwa bayan makaranta da harkar kasuwancinsa?.          Duk yanda taso fahimta ko gano hakan ya gagara, babu kalar dabaru da maman Aaida bata koya mataba duk kuma ta bisu daki-daki amma ta gaza samun haske. A yanzu haka wata ƙura ta fahimta baibaye da ita game da mijin nata shine dalilin kaiwa da kawowar tata.        Tun daga randa Abdallah ya fara kusantarta ba'a cikin hayyacinsa ba a washe gari ya haɗata da wasu ƙwayoyin magani guda biyu. Daga haka kuma duk sanda zai kusanceta sai ya batasu ta sha. Tun bata taɓa kawo komai a ranta game dasu ba harta fara zargar wani abu. Ba komai ya kawo mata zarginba kuma sai haihuwa da akullum maman Aaida ke kawaɗaita mata ta sanadinta zata iya samun soyayyar Abdallah, tunda sunyi dukkan wasu dabaru yaƙi hawa network. Da farko Adawiya batason ta haihu yanzu, amma da taji wannan magana daga maman Aaida sai taji ƙwaɗayin hakan itama dan tana masifar son Yah Ab. To amma sai me? Har yanzu babu ciki babu alamarsa a gareta, har zuwa asibiti tayi a ɓoye aka dubata Doctor ya tabbatar mata inhar bata daina sha maganin hana ɗaukar cikiba bazata taɓa samun ciki ba.       Wannan magana ta daki zuciyarta, dan a ɗan hasashenta ta fahimci kenan maganin da Yah Ab ke bata kullum na hana ɗaukar cikine? Duk da zuciyarta taƙi aminta da hakan sai taji tana ƙwaɗayin dubawa ta tabbatar. Wannan shine dalilin kai kawonta tana nazarin hanyar data dace tabi wajen binciken maganin a ɗakinsa batare daya saniba ko ya ganta. Saboda haka taƙi zuwa makaranta yau ta zauna gadin fitarsa. Sai dai kuma har yanzu bataji ko motsin alamar zai fitoba balle tayi tunanin fitar tasama kamar yasan mi take shirin yi.... (Humm muje zuwa baby Adawiya😉😂). ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼. Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 _______________________ ________________________           Dr Yoohan ya bama matar da yazo kano dominta dukkan gudumawar data dace har ALLAH ya bashi nasarar dai-daita komai da taimakon Dr Aysha. Sai dai fa Dr Sa'ad yasha masifa dan tabbas harda sakacinsa. Ba komai ya sashi sakacinba kuma sai kasancewar matar talakace, hasalima Dr Yoohan shine ya biya mata kuɗin aikin dukda kuma shine yayi aikin. Ya kuma bama marayun ƴaƴanta wasu ƴan kuɗaɗe tare da buƙatar takardun makarantar babban yayansu dake riƙe da gidan da ƴar sana'arsa ta saida ruwa a cikin kasuwa. ALLAH ya taimakesa tun mahaifinsu nada rai ya haɗa diploma ɗinsa da ƙyar da siɗin goshi. Wannan alkairi nasa a garesu ya sakasu cigaba da jera masa addu'oin fatan alkairi da nasara a rayuwarsa. Tare da fatan ALLAH yasa yanada rabo cikin addinin islama.       Tunda Dr Sa'ad yaga Dr Yoohan ya wuce sai ya fara sakaci da kula da matar yanda ya kamata saboda takaicin ƴarta data bijire masa tun farko. Da farko shine zaima matar aiki akan matsalarta, ya buƙaci kuɗaɗe masu nauyi daga wajensu na aikin amma suka tabbatar masa basu dasu. Sunta roƙonsa ya taimakesu ko rabi su bada kafin ta warke sai su cika ya nuna bazai iyaba, sai kuma ya koma ta bayan fage ya nema yarinyar matar akan inhar zata bashi kanta shiko zaima mahaifiyarsu aiki ƙyau bama sai sun biyaba. Itako tace bazata aminceba, dan ran mahaifiyarsu a hannun ALLAH ya ke, sun kuma dogara da shi.        Wannan shine farkon matsalar. Lokacin da Dr Sa'ad ke bibiyar yarinyarnan saiko karaf a kunnen Dr Aysha, hakanne yasa ta koma a ɓoye ta kira Dr Yoohan da roƙon ya taimaki yaran inhar yanada halin yin hakan. Da yake tasan yana Abuja yana hutun kwanaki uku. Sanin ƙyaƙyƙyawan halin Dr Aysha ya saka Dr Yoohan yarda ya baro Abuja ta mota ya nufo kano. Da taimakonta sukaima matar dukkan hidima, ya tafi yabar amanar kulawarta a hannunta ita da Dr Sa'ad. dan Dr Aysha ta ɓoyema Yoohan sunansa dan kare masa mutuncinsa.          Da Dr Sa'ad ya fahimci Dr Aysha ta ɓoyema Dr Yoohan sunansa da ainahin gaskiya sai yay shirin ɓata aikin da akaima matar saboda jin zafin rashin haɗin kai da bai samuba na yarinyarta. Dr Aysha dake taimaka musu kuma data fahimci hakan ta tabbatar masa saita sanarma Dr Yoohan ɗin komai. Wannan shine yay masifar tada hankalinsa kafin ta sanarɗin shi ya kira ya sanar.                 Yunwa da gajiya taima Dr Yoohan rumusu zuwa yanzun, haka ya fito a matuƙar wahale Dr Aysha biye dashi tana masa bayani akan nasarorin da suka samu game da sauran aikin da yayi a wancan zuwan kafin yima wannan matar aiki. Sosai yaji farin ciki a ransa, dan haka ya biye mata suka shiga zagaya ɓangarorin da marasa lafiyar suke yana dubasu.      Duk inda ya gitta addu'a ake binsa da shi, duk da wasu da an masa addu'ar zakaji sunce. Arne ne fa. Jin hakan kansa wasu jikinsu yay sanyi. Wasu kuma suce dan arne ne baza'a masa addu'a ba bisa ga ƙyautatawarsa?.      To shidai baimasan sunayiba, dan farincikine shimfiɗe a ransa ganin nasara na kuma ziyartar aikinsa a koda yaushe. Amma duk da wannan farin ciki sam babu fara'a kota sisin kwabo a fuskarnan tasa saboda halittarsace haka rashin fara'ar.         Suna kammala zagayawa ya kalli agogon dake a tsintsiyar hannunsa. Ganin yaci a wanni uku a cikin uku da rabi na hutunsa ya sauke ɓoyayyen ajiyar zuciya. Bashi da tabbacin samun jirgi mai komawa Lagos yanzu, dan haka ya yanke shawarar nufar Abuja a mota kawai, sauran patients ɗinsa kuma sai dai Richard ya dubasu.      Da wannan tunanin yayma su Doctor Aysha sallama ya fito batare da ko office ɗinsa yay tunanin shiga ba. Amma duk da haka sai da Doctors ɗin dake matuƙar yinsa suka firfito suka gaishesa, sannan suka yo masa rakkiya zuwa wajen guards ɗinsa da basuyi tunanin fitowar tasa ba a yanzun. Dan Solomon suke ta bama labarin abubuwan da suka faru game da kama Nu'aymah da aka turosu yi.                   Cike da farin ciki Solomon ke wata shegiyar dariya, ya ƙyalƙyale da ita yana faɗin, “Inason kafin kuje abuja da ita kuci ubanta a hanya ta ƙarasa da ƙafa ɗaya. Kai bama nason taje da numfashi gaba ɗaya. ku kaita da rabin rai yanda oga zai ƙarasata da kun isa, dan bana fatan kafin mu dawo Abuja boss yaji koda ɓurɓushin labarin abinda ya farune. Kunsansa ɗan hana ruwa gudu ne. Shi a dole masoyin ƙ..........”          Da sauri Solomon ya haɗiye sauran maganarsa jin ƙamshin turaren Dr Yoohan ya cika wajen. Yay azamar juyawa kamar yanda suma sauran duk suka juya a tsorace.      Ganin yana maganane da Doctors ɗin da sukai masa rakkiya ya sakasu sauke ajiyar zuciya. Dan sun tabbata baiji komaiba.            Dr Yoohan yay sallama da abokan aikinsa kafin ya shiga motar da aka buɗe masa yana nai ɗaga musu hannu hamar yanda suke ɗaga masa. A haka motocin suka fito daga cikin asibitin.         “Sir! Zamu koma airport ne?”. Cewar Solomon fuskarsa ɗauke da murmushin jin daɗin kama Nu'aymah da har yanzu ya gaza barin fuskarsa.       Shiru Yoohan ya musu tamkar bai jiba, yama maida hankalinsa kan files ɗin daya fiddo a jikkarsa yana dubawa. Sake maimaitawa Solo yayi.      Nanma sai da yaja wasu sakanni kafin yace, “Police station”.         Ji kake ƙiyyyyy!!! Driver ya taka wani uban birki a firgice, tare da haɗa baki shi da Solomon waje. faɗin, “Police station kuma sir?!”.          (🙄🙄😏An yanka ta tashi ko masu gadi?).        Idanu ya zuba musu na wasu sakanni fuska a matuƙar ɗaure. Sai kuma ya ɗauke kansa ya cigaba da abinda ya keyi. Ganin gaba ɗaya wutar kansu ta ɗauke a fusace ya sake kallonsu “Kona canja yaren da nai maganar da shi ne bakuji wannan ba?”.          Da sauri suka shiga bashi haƙuri, driver ya ƙarama mota gudu zufa na keto masa ta ko ina a sassan jikinsa. Kai kace motar babu ac. kallo ɗaya zaka fahimci tsagwaron tashin hankali da ɓacin rai tattare da su. Driver bashi da wata hanyar daya wuce ya ɗauki hanyar police station ɗin da suka bar Nu'aymah. Acan kuma ƙasan ransu shi da Solomon tunanin mafita sukeyi.     Sunci rabin tafiya wani dabara yazoma Solo a rai, dan haka ya ɗauka wayarsa ya rubuta text ya turama Madam Chioma. Mintuna uku ba'ayi cikakkuba sai ga kiranta ya shigo wayar Yoohan.      Idanunsa ya ɗago daga abinda yakeyi ya kalli fuskar wayar. Duk da yaga sunan Mom ɓaro-ɓaro a jiki sai ya ɗauke kansa ya cigaba da abinda ya keyi. Kiran ya yanke wani ya sake shigowa. Yanzun kam maimakon kallon wanene sai ya lumshe idanunsa ma, sai da sukai kusan sakan goma a rufe sannan ya buɗesu akan su Solomon dake a gaba suna addu'a da fatan ya ɗaga wayar kafin su isa station ɗin.        Lip ɗinsa na ƙasa yaɗan lasa da harshe ya sake maida idanunsa ya lumshe bayan ya kife wayar alamar dai bazai ɗaga ɗinba..         “S...S sir ana kiran wayarka fa”. Solomon ya faɗa da rawar baki.         Tamkar yayi magana da dutse, dan Yoohan yi yay kamarma bai jisa ba, kuma sarai yaji miya faɗa ɗin.        A haka suka iso station ɗin, bai fitaba sai da yaja wasu mintuna, ta cikin motar ya gama ƙarema station ɗin kallo har su Solomon da suka fita suka buɗe masa. Solomon yay ƙasa da kansa ganin banzan kallon da Dr Yoohan ɗin ke masa. Batare da yace da shi uffanba ya zuro ƙafafunsa ƙasa ya fito. Gaba yay suka take masa baya kowanne zuciya babu daɗi.             Duk da ƴan sandan basusan wanene shi ɗinba shigarsa da waɗanda suka rufa masa baya ya sanar dasu ogan gayunne gaba ɗaya. Suda ya kamata ya fara gaidawa sai gasu suke masa tarba cikin tsantsar girmamawa kai kace wani babbane a cikinsu.            Ransa dake a ɓace da guards ɗinsa ya sakashi ɗaga musu hannu kawai batare da ya cire ko baƙin glasess ɗin idonsaba ya buƙaci a kaisa office ɗin d.p.o. Guards ɗinsa zasu magana da nuna masa sunada power ɗin shiga kai tsaye basai an nema masa isoba yay saurin ɗaga musu hannu suma cikin fushi. Tsitt sukayi kuwa kowa kai a ƙasa.             Maida dubansa yay ga ƴan sanda ya sake sanar musu su nema masa iso office ɗin d.p.o. Babu musu suka amsa masa cike da girmamawa, yayinda ɗaya a cikinsu ya nufi Office ɗin d.p.o ɗin domin sanar masa.          “Ranka ya daɗe yace ka shiga”. Ɗan sandan ya faɗa da harshen hausa yana ɗan risinawa. Ko motsi Yoohan baiyiba. bai kuma nuna yaji mi ɗan sandan ya ceba. Wani cikinsu dake acan gefe daya fahimci Yoohan baya jin hausa yay saurin sake maimaita abinda ɗan uwansu ya faɗa da turanci. Sai lokacin ne Yoohan ɗin ya motsa tare da ɗaga musu hannu.           Da sauri Solomon ya buɗe masa ƙofar office ɗin ya shiga. D.p.o yay azamar ajiye biron hannunsa yana mai miƙewa cike da tsagwaron mamakin ganin wanda baiyi zato ko tsammani ba. Shi kansa Yoohan ɗin tsaye yayi kawai yana kallonsa, a ransa yana raya ashe papa yayi amfani da wanda ya sanine shiyyasa ya nuna ƙarfin ikonsa.......           D.p.o ya katse tunaninsa da faɗin, “Oh God! Dr Yoohan!”. Hannu Yoohan ya saka ya zare glasess ɗin idonsa, batare da ya amsa d.p.o ba ya zuba masa idanu kawai kamar mai nazari. Har inda yake d.p.o ya ƙaraso shi, ya nuna masa kujera cike da girmamawa yana faɗin Please Sir ka zauna, ka taimakeni ka zauna”.      Kamar bazai zauna ɗinba, sai kuma miya tuna oho masa sai ya zauna a kujerar da d.p.o ya gyara masa tare da harɗe ƙafafu ya ɗora glasess ɗinsa saman table ɗin.     D.p.o daya koma tamkar ya mance da matsayinsa da kansa ya buɗe fridge ya ɗakko ruwa da lemo da kofi ya ajiye saman table ɗin. Abin mamaki duk ya wani rikice.               Nu'aymah na zaune a office ɗin ta cusa kanta cikin ƙafafunta dake mata wani irin ciwo taji takun shigowar mutum office ɗin. Yanda taji D.p.o na magana ba ƙaramin takaici ya bataba. A ranta rayawa take ‘Shin sai yaushene wai ƙasarnan tamu zata gyarune? Sai yaushene jami'an tsaronmu da duk wasu ma'aikatunmu zasu daina fifita masu hannu da shuni akan talaka? Ta taso gidan da Alhmdllh akwai arziƙi da wadatar zuci, akwai kuma kima da daraja na babban gidan. Dan haka duk inda suka tsinci kansu da wuya kiga ba'a girmamasu, sai dai idan ba'asan su ɗin su wanene ba. Ta tabbata wannan d.p.o ɗin inda ace bahaushene da babu yanda za'ai ya kasajin kunyar tura yaransa har gidansu ɗakkota, koda kuwa za'ace an basa kuɗin toshiyar baki. To amma yanda akema talaka na sosa mata zuciya da ruhi. A yanzu haka shigowarta station ɗin nan taga abubuwa kala-kala da suka sosa zuciyarta duk kuma an yisune akan talaka’. Batare data saniba tsaki ya kufce mata, cikin zafin zuciya da takaicin d.p.o ta ɗago dan taga wane shashasha ne yazo ake masa wannan tarbar tamkar wani IG ko gomnan kanon ma gaba ɗaya.           Akan bayansa ta sauke idanunta, dan ya juya mata bayane bata ganin fuskarsa, ta zuba ma bayan nasa harara duk da bawai ta gane wanene ba.     Yoohan da baisan Nu'aymah nayiba ya kalli d.p.o fuska babu walwala yace, “Inason ka saki yarinyar da papa yasa aka kawo nan”. “Sir amma.....” hannu Yoohan ya ɗaga ma d.p.o da sauri. “Emanuel! Haka kawai nake buƙatar ayi”.        “Za'ayi yanda kakeso sir, sai dai nima ka saurareni ko kaɗanne Please ”. Shiru Yoohan ɗin yayi alamar ya bashi dama. D.p.o daya fahimci hakan sai ya gyara zama, cikin kwantar da murya yace, “Ka taimakeni ka kira Pastor ka sanar masa kaine ka bada umarnin a saketa kar yaga kamar na saɓama umarninsa rayuwata ta shiga garari.      Lumshe idanu Yoohan yayi, wani irin takaici da ƙunci na daɗa faɗaɗa a cikin ransa. Yanajin zafi da matuƙar damuwa idan yaga yanda mutanensu ke masifar tsoron papa. Yakan rasa minene dalilin hakan? Dan kawai yana pastor ne ko me? Kodai akwai wani abu da bai saniba game da mahaifin nasa ne? K........’       “Please sir!”. Maganar d.p.o ta katse masa tunani. Maimakon ya amsa zai kira Papa, sai yace, “Ina yarinyar take?”. Da hannu D.p.o yay masa nuni da Nu'aymah dake bayansu ta sake duƙar da kanta saboda ƙafarta. Kafin Yoohan yace wani abu d.p.o ya bata umarni akan ta taso. Ko motsi bataiba dan abinda ya dameta shine matsalarta ba tsawarsa ba. Yunƙurawa ɗaya daga cikin yaransa yay a fusace zaije gareta Yoohan ya ɗaga masa hannu. Komawa yay ya tsaya inda yake cike da takaici.      Nu'aymah da duk tana jinsu bata motsaba, sai da ƙafarta ta lafa mata. Ƴar sandan da suka ɗakkota a gidace ta shigo bisa umarnin d.p.o ɗin ta taimaka mata ta miƙe. Miƙewar tata tayi dai-dai da ranƙwafawar Yoohan da ya miƙe yana faɗima d.p.o “Police ɗin da suka ɗakkota su maidata, su kuma bama iyayenta haƙuri da wanketa, inba hakaba Emanuel kaine zaka ɗauki laifin”. Da sauri d.p.o ya ɗaga masa kai zufa na keto masa. Yoohan ya ɗauki glasess ɗinsa ya juyo zai saka a ido. karaf suka sauka akan Nu'aymah dake tsaye tana binsa da wani shegen kallo na fusata, dan ko kaɗan batai tunanin shiɗinne yasa a kawota nan wajenba, saboda sam bata wani gane guards ɗinsa ba, hasalima ta manta da shi da abinda ya faru tsakaninsun.      Nunashi tai da ɗan yatsa babu alamar koda tsoro tattare da ita, “Kai ne dama kasa a kawoni nan wajen?” tai maganar fuskarta ɗauke da murmushin takaici, sai kuma ta haɗe fuska da maida dubanta ga d.p.o. “Yallaɓai ai bani na cancanci zuwa nanba wannan mai suffar ƴan damben ne, dan haka nima yanzu na kawo ƙararsa”.       Kafin d.p.o yace wani abu ta fisge hannunta daga na ƴar sandar ta fice a office ɗin da ɗan sauri duk da tana ɗingishi. Saurin bin bayanta d.p.o da ƴan sandan da ke office ɗin sukai, yayinda Yoohan ya lumshe idanu da saka glasess ɗinsa da ganinta ya hanashi sakawa ɗazun shima yabi bayansu.      Isowar su d.p.o yayi dai-dai da furucin Nu'aymah dake tsaye gaban ƴan sandan dake wajen kanta  . “Yallaɓai na kawo ƙara”.       A tare suka kalleta, ɗaya a cikinsu yace, “ƙarar wa? A kanmi kuma?”. Juyawa tai inda su d.p.o ke tsaye cike da al'ajabi da mamakinta, dai-dai kuwa da fitowar Dr Yoohan daga lungun da office ɗin d.p.o yake ta nunasa da faɗin, “Ƙarar wannan mai siffar ƴan damben na kawo”............✍ 😂Wagga ɗiya kina da tsaurin ido aradu😚🚶🏻.                  Barka da juma'a😘😍🤗. _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[4/7, 10:38 PM] Amina Mama: No. 23 ................Tun sakkowar Yoohan daga sashensa Momy tai saurin ajiye kofinta na barasa, dan Yoohan ya daɗe da hanata shan giya, kuma ta masa alƙawarin dainawa. Sai dai wani lokacin damuwar da take ciki kansa tasha abinta musamman da daddare idan zata kwanta barci. duk da dama wani mai yawa take sha ba. Binsa tai da wani shegen kallo tamkar idanunta zasu faɗi ƙasa, yayinda fuskarta ma ta nuna shauƙi sosai fiye da yanda suke zaune. Yunƙurawa tai zata tashi amiyarta madam Monecca tai saurin riƙe mata hannu tana girgiza mata kai cikin hikima. Duk da bataso hakanba saita koma ta zauna tana sauke wasu tagwayen ajiyar zuciyar da harsu Papa da fira ya ɗaukema hankali basusan da wucewar Yoohan ɗinba suka juyi suna kallonta.           “Lafiya Darling?” papa ya faɗa cike da kulawa a gareta. Murmushi yaƙe ta masa da cewar “Babu komai, bara naɗan rage kayana dai sun fara min nauyi”. Murmushi yay mata da aika mata kiss daga inda yake. Ta miƙe tana fadin, “Thanks Honey”.        Rakata da idanu yay cike da so da ƙauna harta haye sama sashen bedrooms ɗinsu. Sai da ta wuce da kusan mintina goma kafin Madam Monecca ta miƙe itama tana neman excuse ɗin zuwa toilet. Duk da kowa yasan dama amintarsu tafi zuwa ɗaya da madam Chioma babu wanda yay zargin komai a sauran matan. Sai ma maida hankalinsu ga hirar mazajen su da sukayi kawai.         A bakin gado Madam Monecca ta iske Momy zaune ta dafe kanta. Ta ƙarasa kusa da ita ta zauna, cikin harshen nasara take tambayarta damuwarta?.          Ɗagowa Madam Chioma tai idanunta cike da hawaye tana kallon ƙawarta, tace, “Monecca! Ina cikin damuwa sosai akan Yoohan, gaba ɗaya ya sake canjamin, ɗan kusancin da nake murnar ya ƙara shiga tsakaninmu a yanzu neman hanyar kakkkaɓar da shima ya keyi. Rungumarsa ma yanzu bayason yaga nayi, sai kiga ya kama ɗacin rai. Nifa na gaji da ɓoye-ɓoyen nan, dan gashi Honey harya fara tunanin wai yay masa maganar aure.…..”        “Aure!?” Monecca ta faɗa cikin tashin hankali.        “Ki bari kawai, jiya da yay maganar naji kamar na bindige shegen nan nama huta da wahalansa, Monecca zan fitoma Yoohan a mutum kawai da buƙatata, duk da kuwa nasan shegen taurin kansa”.         Cikin sauri Madam Monecca tace, “Karkiyi haka, dan zaki samu babbar matsala. kidai bari muyi tunani akai. Wai ita Mira bazata koma gidansu ba ne. sai naga kamar itace ke ɗauke masa hankali?”.         Cikin dariyar da Madam Chioma batai niyyar yiba tace, “Miracle fa? An gaya miki kalloma ta ishesa ne a gidan nan. Dama fa Zamani ne keta son ganin Yoohan ɗin ya aureta. kuma ni na gama fahimtar shima akwai tasa manufar akan hakan, shi kuma Yoohan ɗin duk da ƙyan Miracle ɗin bata gabansa shiyyasa nima zamanta a gidan bai taɓa damunaba”.      Ɗan taɓe baki Monecca tayi tana hararar Madam Chioma a kaikaice. a ranta kuwa rayawa take duk rintsi saita bi hanyar mallakar Yoohan ɗin, dan itama wani Masifaffen sonsa take, tana dannewa ne a gaban ƙawar tata kawai. Sun tattauna sosai ta yanda suke ganin ya dace a samu Yoohan ɗin a hannu. Kafin su fito wajen sauran ƴan uwansu a cigaba da hira.       Haka gidan ya cigaba da karɓar baƙi har dare, dan yau ranace ta ziyara a garesu, musamman ma gidan papa daya kasance babban mutum a wajensu.      Yoohan bai dawo gidanba sai yamma lis, ya samu giyar dasu Osen suka sha ta ɗan sakesu, harma sun fito daga sashensa Solomon ya shiga ya gyara. Duk suna harabar gidan zaune dan wasu abokan nasu sun ƙaru saboda jin Yoohan ɗin na gari, shima sai kawai ya zauna a wajensu duk da ba firar yakeba sosai. ______________________________                 *_SAUDIA_*      Duk da Adawiya na ƙoƙarin ɓoye halayenta hakan bai hanata sakin layi a wasunl lokutan, dan babu abinda ke sakata takaici da ƙunar zuciya kamar yanda Nu'aymah taƙi nuna damuwarta akan duk abinda take mata. Gaba ɗaya Nu'aymahr ma ta maida hankalinta ga ibada ne kamar yanda ta ɗauro niyya tun daga gida.      Tayi mugun yin watsi da shirmen Adawiyar dan ta gama karantarta tsaf akan lamarin nata, to dama tasan tun suna secondary ma Adawiya tasha haɗata faɗa da ƙawayensu, ta kuma koma ta noƙe ta nuna ba ita tayiba. Amma sai bata taɓa nuna mata ta gane komaiba akan hakan, dan duk sanda taje ta sanarma Umm Adawiya ta mata kaza sai Umm ta lallasheta da nasiha da nuna mata muhimmancin haƙuri da ɗan uwa. Hakanne ke daƙile Nu'aymah daga ramuwa ga Adawiyar gashi har hakan ya zame mata jiki.          A wannan tsukun kuma data fahimci Adawiya ta canja sabon salon halaye sai itama ta canja takunta a kanta tana binta da gashi cikin ruwan sanyi, a ranta tana zargin kenan dama Adawiya na son Yah Ab komi?. A duk sanda tai wannan tunanin takanyi ƙoƙarin ganin ta ƙaryata zuciyarta, dan bata taɓa ganin alamar hakan ba ga Adawiya a dacan baya. A ganinta yanzu dai daɗin aurene yasa take ganin tafita kusanci da Abdallahn shiyyasa take shirya yaƙarta a kansa.        Yau ma kamar kullum Nu'aymah na ɗan yin barcin rana a falo, dan da daddare tafi maida hankalinta ga ibada ne, Abdallah ya shigo gidan. Adawiya ta wuce makaranta. daga hajjo sai Nu'aymah. Da tare suke da Hajjon a falo zaune suna ɗan hira sai barci ya kwasheta, itama hajjon saita nufi ɗaki ta kwanta danta huta.          Kafe Nu'aymah da idanu Abdallah yayi ko ƙyaftawa ba yayi, ya ƙaraso inda take yay tsaye kanta yana cigaba da kallonta tamkar mai nazarin wani abu. Cikin barci Nu'aymah taji alamar tsayuwar mutum a kanta. A ɗan firgice ta buɗe idanu saboda barcin nata baiyi nisaba sosai. Ganin Yah Ab tsaye a kanta ya sakata sake zabura tana binsa da kallon tuhuma itama. Sai kuma ta kumbura baki tana ɗauke kanta cike da takaicinsa.         Fuskarsa a haɗe ya zauna a kujerar da take kwance, hakan ya saka Nu'aymah saurin miƙewa sosai tana faɗin, “Yah Ab minene haka wai?”.         “K kika cancanci wannan tambayar ai?”. Ya faɗa shima yana miƙewa yasha gabanta fuskarsa a haɗe, ya cigaba da faɗin, “K harkin isa ki dinga wulaƙantani akan wani banza can Nu'aymah? Kinzo inda nake amma sai wani basar dani kikeyi”.        Cikin rashin fahimta take kallonsa, kamar zatayi magana sai kuma ta fasa ta raɓashi zata wuce. Sake shan gabanta yayi yana mazurai, “Nabaki izinin tafiya ne?”.      Idanunta cike da ƙwalla tace, “To idan na zauna mizan maka? Kodan kaga nazo na zauna a gidanka kakeson ƙuntata rayuwata?”. Hannu ya ɗaga tamkar zai ƙwaɗa mata mari sai kuma ya fasa ya dunƙulesa yana taune lip ɗinsa jikinsa na tsuma. Yace, “Uban wanene Ameer?”.            Cike da takaici Nu'aymah ta kallesa ta watsar, kamar karta bashi amsa sai kuma mamakin abin nasa yasa ta kallesa da ƙyau. “Ban gane mikake faɗa ba Yah Ab?”. A hasale yace tayaya zaki gane mara mutunci. Nu'aymah wai harni zaki iya gudammawa a daren aurenmu saboda wani jaki? Kinsan baƙya sona miyyasa kika yarda aka saka mana ranar aure?”.         Sallamar Adawiya da batai zato ko tsammanin Abdallah zai dawo gidan a wannan lokacinba ya hana Nu'aymah da mamaki ya kume bashi amsa. Turus Adawiyan tayi tana kallonsu, dan wanda bai saniba zai ɗauka ne wata maganar arziƙi sukeyi da juna.      Binsu take da kallo tamkar idanunta zasu zubo ƙasa, Abdallah yay ƙaramin tsaki yana barin wajen ya nufi ɗakinsa. Har Nu'aymah ta cira ƙafa itama zata bar wajen Adawiya ta dakatar da ita ta hanyar riƙo mata hannu. Juyawa tai tana kallonta fuska a haɗe sosai, “Malama sakeni”. Nu'aymah ta faɗa a hasale.       “Anƙi a sakekin, idan kin isa kiyi duk abinda zakiyi. miya haɗaki da mijina?”. Kallon tsantsar mamaki Nu'aymah kema Adawiya, sai dai kuma a fili saita saki lallausan murmushi da har ya bayyana haƙoranta. Tace, “Tunda kinsan mijinkine mizai hana shi kije ki tambayesa miya haɗashi dani? Inaga kamar hakan zaifi birgewa a gareki shashasha kawai”. Ta ƙare maganar da fisge hannunta tai gaba tabar Adawiya da huci.         Hajjo data hango tahowar Nu'aymah saita saki labulen cikin ɗakin ta zauna a bakin gado. A haka Nu'aymah ta shigo ta sameta. “Hajjaju kin tashi ashe?”. Nu'aymah ta faɗa tamkar babu wani abu daya faru. Murmushi Hajjo tayi tana kallonta, “Ba dole na tashiba tunda kin gaza zuwa ki tadani mu wuce massallaci”.      Kusa da ita ta zauna tana dariya, “Ho hajjonmu, yanzu kuma dana tadakin cazaki ban barki kin rintsa ba, gara mu maidake da ƙwarinki karsu Abba suga kin sake rugurgujewa”.       Duka Hajjo ta kaima Nu'aymah da filo. Hakanne ya sakata tashi ta shige bayi da gudu tana dariya. Cike da tausayinta Hajjo ta sauke ajiyar zuciya, a ranta kuma tana ƙulla abubuwa da dama game da rayuwar Nu'aymahr            A falo kam Nu'aymah na shigewa Adawiya ta nufi ɗakin Abdallah a fusace, babu ko sallama ta tura ƙofar ta shiga. Sai dai ganinta yay kawai a kansa kamar an jehota. Kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. Hakan ne ya sake hasala mata zuciya, sai ta fashe masa da kuka. “Yanzu Yah Ab abinda kakemin kana ganin adalcine? Ni dake matarka baka da lokacina amma kanada lokacin dawowa gida da wuri dan ka kasance da Aymah? Badan ALLAH yasa yau na shigo gidan da wuri ba bama zansan hakan na faruwaba tsakaninku. Shin wai da mi Nu'aymah ta fini ne? Wlhy sai ALLAH ya sakamin duk cin amanata da akeyi, kuma ni na gaji zan kira baba malam na faɗa masa komai tunda naga ita hajjo goyon baya take baku ma, ƙilama wataran a gabanta zaku shiga ɗaki ku rufo bazata tankaba saboda tana tsoronku......”         Wani wawan mari ya sauke mata a fuska da saida taga stars na mata kaikawo, balle dama ga azumi. A take ta zube ƙasa da sakin wata ƙarar kuka data kai har kunnen Hajjo.         “Kai Abdillahi lafiya kuwa? Mike faruwa hakane nakejin kukan Adawiya?”. Ta ƙare maganar tata dai-dai lokacin da take ƙarasowa cikin ɗakin. Ganin Adawiya kwance ƙasa dafe da kunatu ya saka hajjo zaro idanu, “Mikai mata Abdullahi?”.      Cikin ɓacin rai yace, “Hajjo barni da ƴar iskar nan kawai, wlhy tai wasa wataran saina karya ƙasusuwanta a gidan nan tunda ita kamar dabba take”.             “Ya isa haka”. Hajjo ta faɗa tana ɗago Adawiya dake ƙasa tana cigaba da sakin gunjin kuka. Saida ta zaunar da ita saman kujera sannan ta sake tambayar Abdallah miya faru?. Faɗa mata komai yayi amma banda tsayuwarsu da Nu'aymah, baisanma ita taji komaiba.      Cikin ɓacin rai Hajjo tace, “Adawiya dama baki da wayo haka? Ita ƴar uwar takice kuma tazama abar kishi a gareki? Har kike jifansu da wannan mummunan lafazin ita da mijinki? Adawiya yaushe kika bari ƙawayen banza suka canja miki tarbiyya ne? Har haka. To wlhy ki shiga hankalinki, idan kuma ba hakaba ni bazan ɗauki wannan banzan halayen a cikin zuri'ata ba, saina ɓatama kowa rai a cikinku har iyayen naku ni babu ruwana. Bandama iya shege kowa na fama da ibadar ALLAH a baki ke kina biyema sheɗan yana ɗoraki akan dokin zuciya. To idan na sakejin makamancin wannan zancen lallai sai kinyi nadama shashasha kawai. Banda ƙaddara da yanzu ita wadda kike cin zarafin ba itace matsayin matar tasa ba”.         Haka Hajjo taima Adawiya tas sannan ta fito ta barsu. Duk abinda akeyi Nu'aymah najinsu, sai dai ko tari bataiba balle a fahimci ta sani ɗin. Daga ƙarshema sukai shiri suka wuce massallaci, suda gidan kuwa sai anyi sallar asuba kuma.       Tun daga wanan ranar Adawiya ta shiga fishi da kowa a gidan. Daga gaisuwa bata sake tankama wani. Ahmad yamata nasiha harya gaji ya watsar da ita shima. Bayan kwana biyu da yay dai-dai da cikarsu kwanaki biyar da zuwa, ashirin kuma ga watan azumi Nu'aymah ta tattara inata-inata ta koma massallaci zaman ittiqafin.        Abdallah yaso hanata, sai dai Hajjo tace ya barta tai ibadarta yamafi zaman nata a gidan aita fitina. Badan yasoba ya haƙura, dan yaso a wannan zaman suyi magana ta fahimta da Nu'aymahr ya samu ya lallaɓa hajjo dasun koma a ɗaura musu aure.         Bayan barin Nu'aymah gidan sai ga Adawiya ta saki jikinta, ashe dama Nu'aymahr ce natsalar rayuwarta. Babu wanda yace mata komai. Saima hajjo ce taima Abdallah magana akan su shirya shi da Adawiyan dan tare zasu wuce Najeriya ayi bikin salla. Kai tsaye Abdallah ya nuna cewar bazaije ba, sai dai Adawiya, dan shi bai manta ALLAH ya isan da mahaifiyarsa tai masa akan zuwan nasaba.       Balbalesa da masifa sosai hajjo tai dan ita batasan dalilinsa na bijirewarba. da taga dai ya tirje ɗin saita kira baba malam ta faɗa masa komai. Shine ya kira Abdallahn cikin bada umarni ya sanar masa ya shirya suzo salla gida tunda suna samun hutu a wannan lokacin.           Abdallah ya shiga tsaka mai wuya sosai akan hakan, dan yasan dai umarnin mahaifiyarsa dana baba malam babu wanda yake da damar tsallakewa a ciki, dan duk sunada daraja da kima a idanunsa da rayuwarsa. _________________________             *_NIGERIA_*       A kwanaki biyun nan abubuwa sun sake tsamari akan Yoohan, gaba ɗaya neman birkicewa yake saboda rashin samun barci, tun daga jiya zuwa yau yaƙi magana da kowa a gidan, yama kulle kansa a ɗaki ya hanama kowa ganinsa. Momy tayi kukan tayi roƙon amma yaƙi buɗewa. Hakama su Gebrail sunyi nasu ƙoƙarin ya sharesu.       Amma saboda ƙarfin hali da burinsa nason cika alƙawari sai gashi a safiyar yau talata yayi shirin tafiya kano. Tunda safe ya bama Solomon umarnin faɗama guards ɗinsa su tafi kano. Su kuma ya nema musu ticket guda uku. Solomon nason tambaya akan hakan yanajin tsoro, dan haka yaja bakinsa yay shiru yaje dai ya cika umarninsa            Kusan ƙarfe huɗu na yamma sai gashi ya sauka ƙasa cikin shigarsa ta suit blue mai haske. sun masa bala'in ƙyau duk da yana a yanayin da a kallo ɗaya zaka fahimci akwai damuwa tattare da shi.       Momy ce kawai zaune a falon sai Victoria da Abraham. Cikin girmamawa a garesa yaran suka shiga gaishesa. Hannu ya ɗaga musu kawai tare da ƙarasowa inda suke duk ya shafa kansu batare da yayi magana ba..      Ya maida dubansa ga Momy da idanunta suka kumbura saboda kuka, ɗauke kanta tayi ita a dole fushi take da shi. Baice komaiba ya ƙaraso inda take ya tsaya a gabanta tare da riƙe kunnuwansa da hannayensa alamar ban haƙuri.      Bata iya dogon fushi da Yoohan ɗinta. Dan haka tai murmushi tare da miƙewa ta rungumesa. Yau dai ya daure bai tureta ba, sai da ta gaji dan kanta ta sakesa sannan, ta amshi tie ɗin hannunsa ta ɗaura masa tana faɗin, “My Boy nikam yaushe zaka fara saka necktie da kanka?”.      Bai bata amsaba, sai dai ya sake ɓata fuska alamar shagwaɓa. Da ƴar dariyarta ta shafa masa kwantaccen sajensa da yasha gyara yau, ya kama hannun nata ya sumbata kaɗan.        “Ina zakaje ma wai?”. Ta tambaya tana tsatstsaresa da idanunta manya. Da ƙyar ya buɗe baki wajen bata amsa da “Kano”. “Kano!! kuma Yoohan? Mizakayo a kano kaida kake cikin wannan halin? Badai aiki ba?”. Kansa ya girgiza mata, batare daya bata wani ƙarin bayani ba yace mata, “Bye” yana nufar ƙofa.         Saurin binsa tai tana kira, amma sai yaƙi tsayawa, saida ta haɗa daɗan gudu ta cimmasa, duk da kuwa tafiyarma ba wani sauri yakeba saboda rashin ƙwarin jikinsa. Yanda ta riƙosanne ya sakashi waigawa ya kalleta. Tace, “Ina tambayarka mizakayo acan amma ka taho baka kulaniba Yoohan”.       Kansa dake faman masa ciwo ya dafe kaɗan, kafin cike da ƙosawa yace, “An gayyaceni ne” danshi baison yin ƙarya a rayuwarsa, kamar yanda ya tsani kuma saɓa alƙawari. Yana gama faɗa ya zare hannunsa zai juya ta kuma riƙewa. Yanzunkam bai juyoba sai da yaja wasu sakanni. Muryarta da damuwa ta zagayo gabansa tana magana. Amma maimakon ya bata amsa sai ya saka yatsansa akan baki yace “Shiii!!!”.        Shirun kuwa tayi tana kallonsa, ya ɗaura yatsunsa saman baki yay mata alamar *_Smile_* kamar yanda ya saba mata aduk sanda ya ganta a damuwa tun yana yaro. Duk da batason yin hakan saita murmusa. Yay mata jinjina yana ɗan lumshe idanunsa dake a kumbure sosai.       Tanaji tana gani ya shiga mota driver ya jasu shi da Solomon suka bar gidan, gashi Papa bayama ƙasar jiya sukai tafiya shi da Uncle Zamani. ★★★★★         Airport driver ya kaisu. inda acan suka haɗu da Manager Hamza Ibrahim yana jiransu. Sun gaisa cikin mutunta juna Hamza na mamakin ganin Yoohan ɗin a ƙunci fiye da waccan ranar. Ga idanunsa da fatarsu tai jajur hakama farar fuskarsa. Haka kawai yaji a ransa akwai abinda ke damun Yoohan ɗin. amma sai baiyi magana ba suka nufi ciki.        Ƙarfe biyar da rabi jirginsu yabar Abuja zuwa birnin dabo kodami kazo mun fika🤗😜.        Kamar yanda Yoohan ya iske Guards ɗinsa na jiransa haka suka iske motoci biyu na tarbarsu kuma. Hakan ya sai ya sake birge Yoohan matuƙa, dan haka bai shiga tasa motarba ya shiga wadda aka aiko musu, Guards ɗinsa kuma suka bisu a baya.............✍   [4/7, 10:38 PM] Amina Mama: *_INA MASU NEMAN INDA ZASU SAMU INGANTATTUN:_* *_HERBALS APHRODISIAC NA GARGAJIYA BANA HADIN BATURE BA MAI SIDE EFFECT..?_* *_TO KU SAURARA KUJI, DOMIN NESA TAZO KUSA.._* *_ZEE HERBALS APHRODISIAC!_* *_ZEE HERBALS APHRODISIAC!!_* *_ZEE HERBALS APHRODISIAC!!!_* *_MUNZO MUKU DA INGATTTUN KAYAYYAKI WANDA ZASU GYARA CIKI DA WAJE_*    *_MUNADA SUPPLEMENT MASU GYARAN JIKI DANA FATA, WANDA ZASA SAKI KIYI SHEKI FATAR KI TAYI LAUSHI. TAYI LUWAI! LUWAI! TAMKAR TA JARIRAI_*     *_AKWAI SUPPLEMENT NA KAYAN MATA WANDA ZASU GYARA KI, KIJI KI TAMKAR BUDURWA, SUPPLEMENTS DINMU BASU DA SIDE EFFECT, DOMIN AN HADO SU NE DAGA INGATTATTUN ITATUWA, WATO NATURAL PRODUCTS NE ACIKI._*        *_KAI BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA, MUNA DA INGATTUN KAYAYYAKIN MATA WANDA KESA KISHIYA KWAFA, WANDA DUK INDA SARAUNIYA TAKAI KIN WUCE, WANDA ZASU TSATSO MIKI MARTABAR KI DA KIMAR KI_*. *_AKWAI INGATTATTUN MAGUNGUNA, NA CUTUTTUKAN DA SUKA SHAFI DAN ADAM DAMA JINNU.. KAI DAMA WANDA BAMU AMBATA BA.. ZEE HERBALS APHRODISIAC (MASARAUTAR INGATTATTUN MAGUNGUNA KENAN)_*      *_KYAU, ARHA, INGANCI, RAHUSA... SAI ZEE HERBALS APHRODISIAC_*    *_MANHAJOJIN MU NA SOCIAL MEDIA: KAMAR INSTAGRAM DA WHATSAPP DAMA NAMBAR TARHON MU: DOMIN SHIIGA KUGA IRIN KAYAYYAKIN MU TUNTUBE MU TA_* _INSTAGRAM LINK DIN MU:_ www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac _WHATSAPP LINK DIN MU:_ https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz _NAMBAR TARHON MU_ 08169380189 *_KARKA BARI A BAKA LABARI GWARA KA BAYAR.. KIZO A DAMA DAKE YAR UWA, KI ZAMO DAYA DAGA CIKIN KASAITATTUN MATA MASU AJI.. MUNA GARIN KATSINA, SANNAN KAYAN MU MUNA BADA SU AKAN FARASHIN SAYA ‘DAI DAI KO SARI.. MUNA TURA KAYANMU A KO’INA A FADIN NAJERIYA._* __________________________________ No. 22 ...............Hankali tashe guards ɗinsa ke kallon juna, kowa nama ɗan uwansa tambaya da idanu dan bakunansu sun musu nauyi har Yoohan yabar sashen church ɗinma gaba ɗaya.     Jigum-jigum sukai da fatan ALLAH yasa ya dawo da wuri kafin madam Chioma ko papa wani ya fito daga cikin church ɗin.      Sai dai kuma addu'ar tasu bataci ba, dan bayan kamar mintuna ashirin da barin Yoohan wajen Rich da ya ga bai dawoba ya miƙe ya biyo bayansa bisa umarnin Madam Chioma. Yanda yaga Guards ɗin sunyi diri-diri da idanu lokacin da yake tambayarsu ina Yoohan ya sakashi daka musu tsawa. Sake rikicewar sukayi, kowa na inda-indar bada amsa. A haka Madam Chioma itama data biyo bayan Rich ɗin ta samesu. Sake ruɗewa sukayi, dan sunsan idanma azaba ce tafi papa akan Yoohan, ga Rich shima ɗan babu sauƙine.     Da ƙyar driver ya iya dauriyar faɗa musu yanda akayi, jikinsa har rawa yakeyi. Yanda Madam Chioma ta rikice sai ka rantse yaronta ɗan shekara biyu ko uku ne ya ɓata. A take ta birkice lissafin Guards ɗin Yoohan da securitys ɗin church ɗinma kansu. Ta kuma tabbatar musu nanda awa biyar idan Yoohan bai dawo ba saisun gane kuransu.       Ana a cikin wannan dambarwar ne aka tashi daga church ɗin. Mutane suka fara tururuwar fitowa suna nufar inda ake rabon abinci. gudun kar ai abin kunya Rich ya shiga lallaɓa madam Chioma akan ta kwantar da hankalinta maybe Yoohan gida ya nufa, tunda duk sunsan a yanayin da yake baya buƙatar kowanne kalar hayaniya. Zata iya yuwuwa ya ƙosa ne da zaman shiyyasa. Da wannan ya samu yaci ƙarfinta suka koma ciki inda suka tarar duk wanda zai fita sai yaje ya jefa kuɗin baikon sa tare da karɓar wani abu da papa ke saka musu a baki sannan mutum ya fice.      Matsawa madam Chioma tai kusa dashi tai masa magana a kunne, kansa kawai ya gyaɗa mata yana murmushi. Ita kuma ta juya ta fito yaranta da su Mira na biye da ita. Koda suka fito sai manyan mata suka zagayeta anata miƙa gaisuwa ga matar Pastor, harma da mazan da matasa kowa burinsa ya gaisheta. Yayinda wasu keta tambayar ina Yoohan dan sun riga duk sun gansa ɗazun. Da yake shi dama zuwan nasa bawani sosai bane saboda yanayin aikinsa sai yazam duk sanda yazo sai su maidashi tamkar wani tauraro mai fitowa a daren sha biyar.       Cike da yaƙe madam Chioma ke basu amsa da cewar wani uzirin gaggawa ya sakashi tafiya, amma wani satin zai tsaya yay gaisuwa da kowa.       Da ƙyar ta samu kanta daga wajensu, gashi rabin hankalinta duk yana ga Yoohan da Rich keta faman kira yaƙi ɗaga waya. Daga ƙarshe ma wayar bata shiga.      Tun shigowar motocinsu ƙaton harabar gidan suka fahimci Yoohan ba gida ya zo ba, dan babu ko mai kama da motar da ya shigo acikin jerin mitocin dake gidan. Sai da suka gama fita sannan Madam Chioma ta ƙwalama maigadi kira cikin ƙaraji. Jikinsa na ɓari ya ƙaraso gareta cikin cika umarni.             Kafinma takai ga jefa masa tambaya Miracle ta rigata. Mai gadi yay saurin basu amsa da cewar Yoohan baizo gida ba. Gaba ɗayansu hankalinsu sake tashi yayi, kowa ya fiddo waya suka shiga nemansa..........😒 🙄😏Mufa an ishemu kamar wani ɗan gwal🤕😤. _____________________________                            Koda Yoohan yabar gidan wani ma'aikata ya nufa, duk da kuwa da ƙyar yake jan motar saboda nauyin jiki dana zuciya da rashin baccin ya haddasa masa.         Yana tsaida motar a inda ta dace ya ɗan kife kansa a sitiyarin motar na wasu sakkani, zuciyarsa ce keta faman masa kai kawo akan abinda yake shirin aikatawa. wani ɓangaren na ƙarfafasa akan dai-dai, wani kuma na raunana masa niyyar tasa. A haka dai ya kwashe mintuna har biyu kafin kiran daya shigo masa waya ya maidashi cikin hankalinsa. Ɗagowa yay a hankali yana yamutsa fuska, ganin mai kiran nashine ya sakashi ɗagawa tana gab da tsinkewa.           “Na shigo” ya faɗa kawai cikin harshen nasara. Bansan amsar da aka bashiba. ya dai yanke kiran tare da buɗe motar ya fita.        Wani matashin saurayi da zasu iyayin sa'anni ya fito daga cikin ginin ma'aikatar fuskarsa ɗauke da murmushi. Kallo ɗaya zakai masa ka shaida shiɗin musulmine, dan yana sanye cikin shadda bara sol dataji ɗinkin tazarce, ga ƙaton tambarin salla a goshinsa ya kuma murza baƙar dara mai taushi.            Tunda ya tunkaro Yoohan ɗin kallonsa yake ta ƙasa ido cike da nazari. amma ba kowa zai fahimci yana kallon nasaba musamman idan akai dubi da yanda yay wata tsayuwar basarwa yana busar iskar dake kaɗawa ta hantsi mai gauraye da ɗumin rana.          “Ina fatan dai baƙo nane?”. Saurayin yay maganar fuskarsa ɗauke da fara'a duk da kuwa tun daga nesa ya gama shaida Yoohan ɗin ba musulmi bane.      Duk da Yoohan yana mu'amulat da musulmai batun yanzuba, a mabanbanta ƙasashe da yarurruka kuma, baya iya sakin jiki da su. Dan shi kullum yana cikin yin taka tsantsanne karsu cutar da shi kamar yanda aka ɗorasa a hakan tun ƙuruciya. Ya dai yarda zai ƙyautatama mai buƙatar taimakonsa ko a wane irin yare yake ko addini, zai kuma gudanar da aikinsa da gaskiya ga kowa. Amma bai aminci da yayi dogon aminci da musulmin ba.       Sai dai kuma gashi yau a karan farko na tarihin rayuwarsa matsashin saurayi ya burgesa, harma da shigar kamalar dake a jikinsa. Duk da babu ɗigon fara'a kota sisin kwabo tattare da shai sai ya jinjina kansa cikin lumshe ido yana mai miƙama saurayin hannu.         Saurayin ya sake faɗaɗa fuskarsa da murmushi yana faɗin, “Ina godiya ƙwarai da amsa wannan gayyata tawa da banyi zaton zata karɓu ba. Sunana Hamza Ibrahim khalil, manager mai aiki a wannan kamfani namu mai albarka”. Yanda matashi Hamza yay magana da harshen ingilishi haka Yoohan dake binsa da kallo kwarjininsa na sake cika masa ido shima ya mayar masa da murtani cikin harshen nasaran. “Dr Yoohan Goshpower”. Ya faɗa a hankali kamar bayason maganar, sai dai hakan bai hana voice ɗinsa mai amo fita da ƙyau ba. “Ina sake godiya da amsar gayyata ta a karo na biyu Doctor”.        “Karka damu” Yoohan ya faɗa a taƙaice. Hamza Ibrahim da kansa yayma Yoohan jagora har cikin office ɗinsa dake a haɗe masha ALLAH, dan babban kamfanine dake fidda kayan masarufi masu ingaci da lafiya ga jikin al'umma.     Sai da Yoohan ya zauna kafin Hamza Ibrahim ya kawo masa lemo, ya tsiyaya a cup tare da ajiye masa gabansa a kan table ɗin. Godiya Yoohan ɗin ya masa. Hamza Ibrahim ya sake yin murmushi yana gyaɗa kansa tare da yima kansa mazauni shima.      Sun sake gaisawa a karo na biyu. Yoohan ya sake bin ba'asin kiran da ya samu daga garesu. Babu wani ɓoye-ɓoye Hamza Ibrahim yay masa bayani cikin nutsuwarsa, tare da miƙa masa envelope yana faɗin, “Wannan itace takardar da suka aiko da ita a baka, abinda yasa ban badata kai tsaye taje garekaba saboda gudun ha'incin mutane, zata iya yuwu akai takardar amma taƙi isa gareka. Shiyyasa na buƙaci dama nazo ni gareka da kaina na kawo maka. Sai ma kace min zakazo da kanka.        Yoohan daya gama duba takardar ya ɗan ɗago kansa yana kallon Manager, kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya haɗiye abinsa a rai yana ƙoƙarin maida takardar cikin envelope ɗin.          Duk da Hamza yayi mamaki da ganin Yoohan ɗin a matsayin wanda yaketa faman hidimtawa bayin ALLAH haka ya haɗiye mamakinsa, dan yayi imani da UBANGIJI na fidda rayayye a cikin matacce, kuma ana samun mutanen kirki a cikin kafiranma, wanda wasu musulman mu sukan gaza gyara zukatansu su zama haka duk da addininmu ya koyar damu komai. cikin hikima irinta masu ilimin addini dana zamani yace, “Yallaɓai ina fatan dai zaka amsa wannan gayyatar? Dan suma mutanene masu karamci da mutunci kamar kai, na tabbata alkairinkane kuma yake sake girmamarsu shiyyasa suka shirya wannan liyafar a gareka domin nuna girmamawarsu a kanka”.       Karan farko a rayuwar Yoohan da kalaman hikima sukai masa daɗi a rai, har yay wani ɗan motsi da laɓɓansa mai kama da murmushi amma ba murmushin bane ba. Idanunsa ya ɗan lumshe na wasu sakanni yana nazari. Ba zuwan bane matsalarsa, ciwonsane damuwarsa. Bayason kowacce kalar hayani, ba kuma ya buƙatar shiga cikin kowanne irin mutane gudun ƙuntatama wani. To amma kuma maganar Manager tai tasiri a ransa harma da tunaninsa.      Buɗe idanunsa yay a hankali ya ɗan gyaɗa kansa, “Babu damuwa zanje ɗin, sai daifa ka shirya ayi tafiyar tare da kai”. “Ni kuma Doctor?”. Manager ya faɗa yana ɗan waro idanu. “Indai kace bazakajeba nima kam zan fasa, dan saboda kaine dama zanje. Banyi musu komai dan su damu da sanina ba, sannan wanna shine karo na farko da aka buƙaci yimin karamcin da bai shafi aiki na ba ko yarena ko addinina ba. Shiyyasa nakeson na halarta ko zai shiga tarihin farko da ƙarshe na rayuwata”.          Manager ya gyaɗa kai a ransa yana faɗin ‘daga ganin wannan a Christians ɗinma inaga ɗan ɗariƙar Catholic ne, ALLAH yasa ina ɗaya daga mutanen da zasu jagoranci duhunsa ya samu haske’ a zahiri kuma sai yay murmushi da faɗin, “Babu damuwa, indai kana buƙatata a tawagar masu rakkiya bazan ƙi ba”.     Hannu Yoohan ya miƙa masa tare da yin godiya, kafin ya miƙe alamar zai wuce dan yasan hankalin families ɗinsa nacan a tashe da rashin ganinsa.      Har mota Manager yay masa rakkiya yana ƙara masa godiya sosai, dan yana cikin mutanen da ayanzu company ɗin ke jin daɗin shigowarsu cikin manyan Customers. ★★★          Lokacin da Yoohan ya iso gidansu ya iske kowa a birkice, dan har papa ya baro church yayo gida. Harma yana shirin kiran police station yay report.      Tun a harabar gidan ya fuskanci akwai abinda ke faruwa a gidan, dan yaga baƙin motoci da yake ƙyautata zaton na Uncles nashi ne. Sannan yanda yaga Guards ɗinsa da sauran securitys ɗin gidan na sauke manya-manyan ajiyar zuciya yasan da walaki. Amma kowa bai tankamawa ba ya nufi ƙaton ƙofar falon nasu na glass da yaja manya kuɗaɗe masu nauyi koda ba'a faɗaba.       Wani ihun farin ciki Miracle ta kurma dan itace ta fara ganinsa, kafin ta kwaso a guje tazo zata ɗane masa jiki. Sai dai yanda ya wani uban tsumewa ya sakata jan birki a gabansa ta kama hannunsa kawai ta ƙanƙame a ƙirjinta. A take sauran yaran gidan da baƙin ƴammata da samari yaran Uncles ɗinsa suma duk suka taso kansa. Basubi takan tsumewar tasaba sukam duk suka rungumesa.      Da ƙyar madam Chioma ta samu suka sakesa, itama ta matsa ta rungume abinta tsam yanda takeso hawaye na gangaro mata akan fuska. Hannunsa yasa ya ɗan buga bayanta kaɗan tare da ɗagota yana mamakin hawayen na miye? Batare da yace komaiba ya ciro handkherchief a aljihunsa ya share mata hawayen.           Ƙarasowar su Papa da Uncles nashi uku yasa madam Chioma matsawa suma duk suka rungumesa, hakama matansu. Shikam dai kansa sake ɗaurewa ya keyi, dan haka ya tambayesu wai ko lafiya?.      Basu bashi amsaba sai da Madam Chioma data kama hannunsa ta kaisa har saman kujera, Victoria ta kawo masa ruwa dan kowa yasan yafi ƙaunarsa sama da kayan zaƙi. Bai musaba ya amsa yasha kusan fin rabi, sannan ya sake binsu da kallo da sake tambayar yaya akayi wai?.        Gebrail ne ya sanar masa da komai. Hakan ya saka Yoohan ɗin dafe kansa dake sara masa kaɗan-kaɗan yana ɗan lumshe idanu. Shi abin nasuma takaici ya bashi sosai. Amma sai baice komaiba. Sanin bazai ceɗinba yasa babu wanda ya damu da jiran sai yace ɗin. Saima ringuɗa da sukai Dining domin yin breakfast ɗin da suka kasa yi tun ɗazun.         Shi dai Yoohan duk a takure yake matuƙa, amma sanin baƙar masifar Uncle Zamani yasa shi haƙura ya zauna akai breakfast ɗin da shi, wanda shi sam ma baici wani abin kirki ba. Bayan sun kammala sukai sama shida sa'anninsa su uku, sai Rich daya dawo daga nemansa. Amma duk masifar da yay masa akan ɗaukar mota ya fita shi kaɗai a wannan halin da yake ciki sai bai kula Richard ɗinba. Shima bayan gama masa masifar sai ya watsar dashi ya biyema su Osen kawai da suka baje a falon Yoohan ɗin suna kwasar dariya da hirarsu ta shaƙiyanci akan ƴammata.       A haka Solomon ya shigo da kwalaben barasar da sukai Order, sai kofuna da ƙanƙara. bayansa cikin ma'aikatan gidanne ɗauke da tray da aka shiryo gasashen naman kaji a cikinsa wanda zasuyi amfani dashi wajan shan barasan.      Sai da suka jera musu komai yanda ya dace kafin su fice su barsu. Miƙewa Yoohan yay zai shige bedroom dan ya rage kayansa. Da sauri Godwin yace, “Mr-x ina zuwa?”. (Dan haka duk abokansa ke kiransa da shi, Rich kawai yafi kiransa da Doctor) Yamutsa fuska Yoohan yay yana hararsa, dan dama abokin bugawarsa ne, kawai dai dan yau baya cikin good mood ne. “Ina zuwa” ya bashi amsa a taƙaice yana shigewa.            “Wai mike damun Boss ɗinka ne?”. Joseph ya faɗa yana kallon Richard.  Cikin damuwa Rich yace, “Matsalarsa ce dai ta rashin barci ta motsa, nayi-nayi yasha barasa ko nai masa allura yaƙi”.          Godwin ne yace, “Shegen taurin kan Mr-X ai ba ƙarewa yakeba, ni wlhy sonake wataran na samu wata na biyata tai disvirgin ɗin gayen nan kozai ware yaji daɗin rayuwarsa. Duniya ai sai da jin daɗi, amma shi yabi ya wani ƙanƙame kansa kamar wanda bai wayeba ko ba'a turai yay rayuwa ba. Minene a giya? Dama da shanta kawai nishaɗine, kuma tunda munada aikin yinmu sai fa lokaci- lokaci muke shanta, ba kuma mai cutarwa ba.......”      Katsesa Joseph yayi da faɗin, “Kaga G. Ka barsa, Mr-x tsarinsa kenan shi da ra'ayinsa, koka manta tun muna secondary shi dama komai nasa da ƙa'ida ya keyi. so ni banga abin damuwa da har zaku shiga masa rayuwa da yawaba, kubarsa ya tsara ma kansa yanda yake buƙatar ya rayu Ok?”.            Richard yace, “Hakane Joseph, amma idan ka lura shima fa bawai jin daɗinne baya buƙata ba, kawai shi dai ya ɗauki burin duniyane ya ɗaura akan aikin nan namu, a tunaninsa duk abinda zai sha zai iya shagaltar da shi akan aikinsa, sannan mata ma zasu iya takura masa su hanashi yin rayuwarsa da ƙyau, kunsan mutum namu ɗan hutune, ko mace bata faɗa masa son jiki ba”.      Dariya suka kwashe dashi gaba ɗaya suna mai haɗa kofunan da suka zubama barasa a ciki alamar chssss.        Hakan yayi dai-dai da fitowar Yoohan daga ɗaki, ya canja kayansa zuwa wando da riga duk blue na kamfanin adidas. Duk da hayaniyar tasu bai sonta haka ya zauna a cikinsu dan gaba ɗayansu childhood Friends ɗinsa ne, kuma ƴan uwansa na jini dan duk ƴaƴan ƙannen papa ne, sai Osen ne kawai ɗan aboki shima kuma iyayen nasu sun zama kamar ƴan uwa, sai kuma Richard shi kuma abokinsa. Amma tare sukai secondary school dukansu, hasalima duk ajinsu guda.      Osen ne ya miƙa masa cup duk da yasan ba sha zaiba. Aiko Yoohan ɗin ya yamutse fuska da girgiza masa kai tamkar mai ƙyanƙyamin giyar ma. Dariya suka sanya masa suna zuba masa shaƙiyancin da suka saba, tare da labarin daɗin da ƴammatansu ke jiyar dasu harma da karuwai dan dukansu ji suke da ƴan kuɗaɗe a aljihu. iyayensu kuma sun tara, sanna suma ɗin gwasaken kansune sosai. Shiyyasa suke zuba tsiyarsu a garin Abuja da Lagos kamar babu gobe.          Duk abinda sukeyi saboda Yoohan yaji haushine yay budurwa, dan har maganar ƴammatansa dake bala'in sonsa suke kawowa harda Miracle, tare da koɗa ƙyawunta dama na sauran ƴammatan da Yoohan ɗin shi yake nuna kullum basa gabansa.          Joseph yace, “Mr-x daga yau ka fara taka tsantsan da G-boy, dan ya shirya yanda za'a maka fyaɗe, kaga sai kasan zaman da zakai da shi”.     Mangare ƙeyar Joseph Godwin yayi yana faɗin, “Munafiki, halan giyan ya fara kai maka karo zaka haɗani da shi”. Dariya suka kece da ita duka. Yoohan dake harar Godwin ɗin yace, “Barma wani kare kanka naji sanda kake faɗa ai, an faɗa maka ni irinka ne da baida damuwa saita kwana da mata. Please, try and change your habit kaima”.      Nanma dariya suka sanya, dan sunsan kam G-boy shege ne akan mata, duk yanda zai yaudareki ya biya buƙatarsa ya sani. Rich yace, “Calm dawn my Doctor, duk randa ya aikata maka haka zuwa zakai kawai ka tona masa asiri wajen babien sa, dama gata da shegen kishi kamar taci wuta a cikinta.......”         Osen dake ƙoƙarin yagar nama yace, “Ashe ka ganota, nifa haushi take bala'in bani, amma G-Boy sam baya ganin laifin hakan da take masa, da kayi magana saiya nuna cewar son da take masa ne”.        Ajiyar zuciya Yoohan da warin giyar ya fara hawar masa kai ya saki, ya miƙe a hankali ya ɗauki basket ɗin da aka zubo musu kwalaban giyan ya nufi hanyar fita. Da sauri suka shiga kwala masa kira akan ya kawo musu abinsu, amma baiko juyoba ya fice yama kullesu ta baya ya sauka ƙasa. Canma iske su Papa yay suna ɗora tasu suna hira da dariya harda su Momy suma sha suke. Sosai ransa ya sake sosuwa, sai kace ba yanzu papan ya gama wa'azi a church ba. Tsaki yay ciki-ciki ya wucesu batare da ya tanka musu ba yana ƙwalama Solomon kira.        Da gudu ya shigo kuwa, ya miƙama masa basket ɗin kawai babu bayanin komai ya fice a falon. Garden ya nufa. Sai dai kuma yana shiga ya hango su Miracle a cikin swimming pool suna wanka. Cike da farin ciki duk suka zuba masa idanu, kowacce kwaɗayinta a kansa na fitowa fili saman fuskarta. sai dai kuma tuni ya juya yana jan wani tsakin takaici. Wannan taron yasa sam bayason zama gidan ranar lahadi, yanzu haka zuwa anjima gidan sake cika zaiyi da wasu baƙin kuma. Solomon ya bama key ɗin ƙofar sashensa daya kulle su Rich, yace yaje ya buɗesu, shi kuma ya fice gidan a ƙafa duk da kuwa rana ta fara ɗagawa kuma akwai ɗan zafi............✍ Amin afuwa jiya ciwon kai ya hanani sukuni na kasa typing ɗin🤦🏻. _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻. [4/7, 10:38 PM] Amina Mama: No. 24 ...............Baba malam daketa kaikawo na ƙoƙarin ganin komai ya kammala yanda yake buƙata ya nufi sashen nasa a karo na babu adadi. Yanda ya hana kansa sakat akan tarbar baƙonsa haka ya hana Umm sakat itama, dan baiwar ALLAH nan tun ƙarfe biyun ran take a kan ƙafafunta tana hidima. Sauƙinta ma Addah ta shigo tana taimaka mata, ga kuma mai aikinta.            Omar ne biye da shi, dama yafi shaƙuwa da shi a samarin yaran gidan fiye da kowa, duk da dai ada kam sunfi shaƙuwa da Abdallah, amma daga baya da Omar ɗin yafi Abdallah zaman kano sai shaƙuwarsu ta zarce ta tsakaninsa da Abdallah ma. Dan shi Omar yarone mai tsananin ƙwazo da biyya ga iyayen nasa, sannan baba malam shine babban malaminsa na addini fiye da kowa, shiyyasa koda yaushe yana kano bai cika son zaman Abuja ba shi.      Kai tsaye kitchen suka nufa, inda suka iske Umm da Addah suma dai kamar su tsinke nasu ran, dan tare suke aikin daya rage ɗin. Bayan Baba malam yay sallama baima bari an amsa masaba yace, “Umm Muhammad yaya kun kammala?”.      Ɗagowa Umm tai taɗan kalli mijin nata, sai kuma ta maida akan aikin gabanta tana cewa, “Abban Nu'aymah wlhy nikam dai zakama sake rikitamu gaba ɗaya, insha ALLAH muna gab da kammalawar, dama zuwa kai kayi wanka dan magrib ta gabato”.      Murmushi shimfiɗe a fuskarsa ya ƙaraso yana amsar abinda take tace lemon mangwaron daya rage su haɗa. “Ke dai kawo na taimaka miki ki kammala kawai, dan yanzu haka an wuce ɗakkosu fa”.      Dariya Umm da Addah da Omar sukai, ya ƙaraso wajen baba malam ɗin yana faɗin, “Abba kawo ni nayi basai kayi da kanka ba. Dan nikam yau namafi kowa zumiɗin son ganin wannan baƙo mai daraja a wajenku Abba, dan naga gaba ɗaya hankalinku na kan son ganin an ƙyautata masa, yau kota abincin buɗa bakinmu bakwayi sai na baƙo”.         “Kace ido ka saka mana? Hakama malam ƙarami (baban yaron Addah) sai da ya gama ƙorafi kafin ya wuce airport ɗakkosu”. Ita dai Umm da Addah dariya sukayi musu kawai, ta matso suka ƙarasa haɗa komai ita da baba malam ɗin. yayinda Omar da Addah kuma suke ɗorawa tray. Omar ne ya ƙarasa kwashewa ya kai komai can sashen kakansu  inda za'a sauke baƙon. Hakan kawai ya isa kasan an daratta baƙon sosai, dan duk baƙon da su Baba malam zasu kai da shigo dashi cikin gidansu to lallai ya isa kuwa.      Sai da yaga an fita da komai sannan ya sauke ajiyar zuciya, tare da ficewa domin aiki da shawarar Umm ta farko. Cike da gulma irin ta aminai Umm da Addah suka kalli juna, sai sukai murmushi kawai dan Baba malam ɗinne ya basu dariya.     Ficewa sukai a tare suma zuwa sashen da aka shirya abincin, suka ƙara gyara komai tare da saka turaren wuta da kuma Air Fresheners masu ƙamshi. Kamar Umm ta sani har zasu fito saita yanke shawarar fita da kaskon turaren, acewarta kar ko a baƙin asamu mai Asthma ya cutu. Ta ɗan ɗaga labulen Windows ɗin kaɗan hayaƙin turaren ya ragu sosai. Cikin sa'a ma sai gashi Omar yaje ya tada Genretor. Ac suka kunna tare da sake duba komai suka tabbatar yayi dai-dai sannan kowa ya nufi part ɗinsa Umm nama Addah godiya.       Dan tasan badan itaba da aikin baiyi sauriba sam. Mama amaryar Abba Musbahu kuwa dama ita sai a hankali ce, San jikinta bai bari tama kula da sashenta ba balle taimakon wani kuma, komai ƴan aikine keyi, kodan taga mijin ba mazauni bane oho.          Motocin na shigowa anguwar ana fara kiraye-kirayen sallar magriba. Yoohan na kwance shiru a jikin kujera idanunsa a lumshe. Baisan inda ake shiga da fita ba har saida motocin suka tsaya a ƙofar katafaren gate ɗin. Hakan sai yayi dai-dai da fitowar baba malam da Abban su Adawiya, sai Malam ƙarami da Omar da sauran samarin gidan da yara amma iya mazan kawai.        Duk da yanda guards ɗin Yoohan suka firfito suka zagaye motar da yake a ciki hakan bai saka fuskokin su baba malam sauyawa daga fara'ar dake tattare da suba. Akan idonsu Hamza Ibrahim ya fita. Kafin Yoohan da Solomon ya buɗemawa shima.      Shima a gaban idanun nasu ya fito, bayan ƙafarsa kuma da sarƙar Cross ɗinsa suka fara cin karo kafin cinkusashshiyar fuskarsa. Abinda zai baka mamaki a tare su baba malam sukayo caa a kansu. Cikin ƙyaƙyƙyawan tsari na masu ilimi da baiwar hikima suka tarbesu. Wani iri Yoohan yaji a ransa shima duk da kuwa dama ya fahimci masu gayyatar tasa musulmai ne, amma sai ya dake ya basar.            Duk yanda yaketa faman musu shan ƙamshi da cika da batsewa babu wanda ya canja yanayin nasa, saima sannu da zuwa da suka shiga jera musu tare da basu hannaye suna musabaha har guards ɗin. Kafin baba malam ya bama Malam ƙarami da Omar damar shiga da Yoohan ɗin ciki. Danshi Hamza Ibrahim ya buƙaci a inda zaiyi alwalane kai tsaye.       Yoohan dai baiyi musu ba yabi bayan su Omar, sai dai idonsa da zuciyarsa nakan hasaso masa a inda ya taɓa sanin fuskar baba malam a rayuwarsa. Guards ɗinma bin bayansu sukai. Omar zaiyi magana baba malam ya girgiza masa kai alamar ya barsu.           Tun a farkon shigowa gidan Yoohan yasan masu gidan sun wuce raini, dan babu abinda nasu gidan zai nuna masa sai dai kayan ƙawa da ƙyale-ƙyale, nasu baba malam ma yafi nadu girma sosai. A haka su Omar suka kaisa har falon, guards ɗinsa biye da dasu kamar wasu jela ko suna ganin za'a cutama Yoohan ɗinne oho musu. Sai da sukaga ya zauna suka ajiye masa ruwa da lemo kozai buƙata sannan sukai masa sallama suka fito, duk da basuji ya amsa musu da ƙyau ba. Dan Solomon ma tunda ya fahimci inda suka kawo kansu sai takaicin ogan nasa da buɗaɗɗen ra'ayinsa ya shiga masa zafi a rai. Dolene yay saurin sanarma Madam Chioma kafin a bama Boss ɗin nasu wani abin yaci a tsafesa.         Yana cikin shawara da zuciyarsa ta yanda zai silalo daga cikin falon ya kira madam ɗinsu sai ga sallamar su Baba malam, da alama ana idar da sallar magrib basu zaunaba suka shigo gidan. Aiko takaici kamar ya kar Solomon, amma duk da haka saida yayi dabarar turama Momy text message ko za'a dace wayar na a hannunta ta gani.          Koda suka shigo Yoohan na'a zaune yanda yake baiko motsaba, sai dai yana binsu da kallo ne ta ƙasa ido. Abban Adawiya da suka taɓa haɗuwa a orphanage ranar da suka buge yaron nan sai ganin Yoohan ɗin ya sakashi matuƙar jin mamaki. Duk da ya jima a ransa yana zargi da hasashen kodai shine mai musu wannan ɗawainiyar. Rashin tabbas ɗin hasashen nasa yasa bai taɓa yin magana ba sai yanzu ya ɗan gwargwaɗa ma baba malam cikin harshen larabci.      Murmushi kawai baba malam ɗin yayi, cike da kulawa ya maida hankalinsa akan Yoohan da suka fahimci a takure yake da kasancewarsa a wajen. Basu damuba, dan sunyi gamo da waɗandama suka fisa taurin kai da aƙida amma cikin amincin UBANGIJI sun sami nasarar canjasu. To balle shi kuma dama suka fahimci zuciyarsa nada rangwame tunda har ya iya kasancewa maison ƙyautatawa marayu.      Duk da baba malam yaga saɓanin abinda yay tammani daga Yoohan hakan baisa ya canja komaiba daga ɗokantuwa da mutunta baƙon nasu. Hakam ɗan uwansa da ƴaƴansu basu nuna wani mamakinsu a fili ba ko ƙyanƙyamin su Yoohan ɗin, kowa ya shanye a ransa. Ba Yoohan kawai ba, dai-dai da guards ɗinsa an mutuntasu fiye da zatonsu, dan suma ca akai su zauna ayi buɗa bakin dasu. Duk da suna noƙewa saboda boss ɗinsu haka baba malam ya matsanta musu. Ganin Yoohan kuma bai tanka musu ba, yamayi kamar baisan mi akeyiba sai suka saki jiki aka kwashi gara da su, a ransu kuma suka koma zuba santi dajin kimar mutanen musamman yanda aka nuna musu suma mutanene masu daraja ba bautace kawai aikinsu ba.       Yoohan kansa da keta noƙewa da farko tuni baba malam ɗin ya tsaresa sai yaci, harda nuna masa idanfa baici da hannunsaba shi zai basa da kansa to, kuma ɗura zai masa. Karan farko a rayuwata da ni kaina mai ɗakko muku rahoto naga murmushi a fuskar Yoohan yau. Dan shi kansa a bazata ya saki lallausan murmushin ga baba malam ɗin.       Baba malam yace, ‘Masha ALLAH’ a ransa, duk da yau ya fara ganin Yoohan sai yaga murmushin yay bala'in masa ƙyau. Haka dai suka gudanar da buɗa baki cikin nishaɗi da farin ciki. Guards ɗin Yoohan dake ɗar-ɗar harda Solomon mai hasashen banza sai gasu sun kwashi gara suna washe baki dajin farin ciki a ransu.     Kiran sallar isha'i ya saka su baba malam ficewa massalaci akabar Yoohan da tawagarsa. Sai dai kuma bayan fitarsu babu jimawa shima sai ya miƙe da nufin ɗan yin tattaki ko cikinsa zai sauka. Shi kansa yasan ya jima a rayuwarsa baiyi irin wannan cin abincinba, ballema a ɗan tsakanin nan da yake cikin halin ha ula'i. Ta ƙaramar ƙofar da yaga su baba malam ɗin sunbi shima ya bi, kai tsaye ta kaisa ƙatuwar harabar massalacin kuwa.          Ko'ina ƙwanyar yake da haske tamkar rana. Ga mutane maza da mata harma da yara cike da massalacin harda mata. Yoohan yay tsaye jikin katanga yana kallonsu cike da nazari har aka tada salla. Ba massallacin kawai ba hatta anguwar kanta sai yaji ta ɗauki shiru gaba ɗaya, babu abinda kakeji sai sautin karatun salla da baba malam keyi. Lokacin da ya kammala karanta fatiha mamu suka amsa da “Amin!!!!” sai gaba ɗaya tsigar jikin Yoohan ta tashi, zuciyarsa tai wani bala'in tsargawa har saida ya rumtse idanunsa.         Baisan dalilin daya hanashi komawa ciki ba, haka ya cigaba da tsaiwa har sukai ruku'u. suka sake ɗagowa sukai sujida. Tsigar jikinsa sake tashi tayi a karo na biyu, dan yanda sukai sujidan gasu a sahu nagartacce dolene ko musulmin ya gani yaji ƙarin imani a ransa balle wanda bai taɓama yin sujudar ga UBANGIJI ba.       A hankali Yoohan ya ɗaga ƙafafunsa ya fara ja baya da ƙyar harya fice a harabar massalacin ya koma cikin gidan. Haka ya cigaba dajan jiki harya isa falon da aka saukesu da ƙyar. Tsitt guards ɗinsa daketa faman surutun santin abincin da sukaci sukayi ganin ya shigo kamar a birkice. Da sauri duk suka miƙe tsaye domin girmamawa. Solomon ya taimaka masa ya zauna.      Sai kuma duk hankalinsu ya tashi, amma yanda baiyi maganaba suma sai basuyiba sukai dai masa tsaye cike da tsoron kodai an cutar dasu ɗinne kamar yanda sukai hasashe tun farko?.         Har aka idar da sallar asham Yoohan bai dawo hankalinsa ba. Baba malam da ayau baije tafsir ba dama ya ɗauki alfarma suka sake shigowa. A yanda yaga Yoohan ɗinne ya saka hankalinsa tashi. Tambayar guards ɗin ya shigayi a ruɗe. Nan sukai masa bayanin abinda suka sani kawai. na cewar Yoohan ya fitane shan iska sai ya dawo musu a haka, dama kuma bashi da isashen lafiya, bama suyi zaton zai iya zuwa nan lafiya lau hakaba.        Ɗan shiru Baba malam yayi cike da nazarin bayanin da Solomon yay masu na rashin yin barcin Yoohan, kafin ya zauna kusa da Yoohan ya janye hannunsa daya dafe kansa da shi ya maye gurbinsa da nasa, addu'oi ya fara masa yana tofawa, ya kuma saka Abban Adawiya yin wasu addu'oin a ruwa ya miƙo masa. Kamar Solomon zaiyi maganar karsu bashi sai dai ya kasa saboda nauyin da bakinsa yay masa da kuma kwarjinin mutanen.        A gabansu akaba Yoohan ruwan addu'ar yasha. baba malan ya zuba a hannunsa kaɗan ya kuma shafa masa a fuska. A take ya fara sakin tagwayen ajiyar zuciya a jajjere. Ya buɗe baki da ƙyar yace, “Thanks”. Murmushi baba malam yayi kawai, kafin yace, “inaga ya kamata a kaiku masauki ka huta, dan da alama idanun nan naka barci sukeji”. Cike da mamaki Yoohan ke kallon baba malam, duk da dai ya kasa yarda su haɗa idanu da ƙyau dan bala'in kwarjini baba malam ɗin ke masa shikam. Sake murmusawa baba malam ɗin yayi. Ya ɗauke kansa ya maida gasu Omar.       “Farukh a kaisu masauki ko”. Da sauri Omar yace, “To Abba”..             Da gaske Yoohan barci yakeji fiye da zatonsa, dan haka ya kasa musama baba malam duk da kuwa shi a yau yaso su juya zuwa Abuja shi da Solomon da Manager, guards ɗinsa kawai yay shirin bari su kwana a kanon da safe suma su wuce. Amma sai yaji babu abinda yafi buƙata kamar kwanciya a yanzun.           Su Malam ƙarami sun kaisu gida mai ƙyau matsakaici dake gaba da gidansu kaɗan, inda nanne masaukin da su baba malam ɗin kan sauke baƙi daman. Tsaf yake gidan, saima uban ƙamshi mai saka kwanciyar hankali da ya keyi. Duk da babu wutar nefa nanma an tada gen.....      Abin mamaki sai ga Yoohan kamar bugagge, suna shiga wajen kwanciya ya buƙata. Yana ganin gado kuwa ya zube akai yana sauke ajiyar zuciya abin tausayi.      Takalma da necktie ma sai Solomon da Manager ne sukai dabarar zare masa. Hakama jacket ɗin suit ɗinsa. Sai suka barsa da shirt ɗin da dogon wando kawai.          Manager ne ya kwana tare da Yoohan duk da shi Solomon baiso hakaba. Bawan ALLAH nan yanda ya kwana bautar UBANGIJI haka ya ja doguwar addu'ar samun haske daga Yoohan ɗin. Hakama su baba malam, ranar mafi yawan addu'oinsu akan Yoohan suka yisu da ga su har iyalansu. Da asuba aka kawoma Hamza abin buɗa baki, daga Yoohan har guards ɗinsa barci suke kwasa masu a lokacin. ★★★WASHE GARI★★★              Washe gari sai ga kowa ya tashi banda Yoohan, barci yake cike da kwanciyar hankali, dan haka baba malam daya zagayosu har sau kusan uku ya hana a tadashi.       An kawo musu lafiyayyen breakfast sukaci suka ƙoshi, wajen sha biyu ma aka sake kawo musu abinci nanma. Ganin har ɗaya saura bai tashiba Solomon ya bama sauran ƴan uwansa shawara akan su tafi, shima zaije ya sayoma Yoohan kaya ya kuma nema musu ticket. .       Basu musama wannan shawara ba, suka shirya suka tafi harda Solomon ɗin, dan sai da suka kaisa ya kammala uzirinsa kafin su sake maidosa gida, sukaje sukai sallana da baba malam da yake a lokacin sun samesa tsaye a ƙofar gidansa ya dawo daga orphanage ne..        Baiso tafiyar tasuba, amma sai bai hanasuba tunda ƙila sunada uziri. Ya musu godiya sosai tare da basu tsaraban da aka shiryama Yoohan ɗin dan suyi gaba da ita, suma kuma aka basu tasu. Yanda su baba malam ke musu godiyar sai duk abin ya ɗaure musu kai da saka jikinsu yin sanyi akan a ƙidarsu. Har suna hasashe a ransu dama haka musulmai keda kirki da karamci amma ake aibantasu da nuna musu suba mutanen kirki bane? To su dai gashi jiyane karon farko da sukai mu'amula da musulmai hausawa mai tsaho amma sai basuga hali mara ƙyau ɗin da ake faɗar suna da shiba saima alkairi da ƙyawawan halayya abin koyi.      Sun tafi da wannan alkairai da akai musu cikin rai sosai.      Bayan wucewarsu baifi da mintuna talatinba Yoohan ya farka. Yayi matuƙar mamakin ganin inda ya kwana, manager ya taimaka masa da ruwan wanka, Solomon zai shiga gabatarma Yoohan ɗin da kayan daya siyo masa sai ga malam ƙarami da kaya sabbi fill ya kawo. Sai kuma abinci da aka shiryoma Yoohan ɗin tunda sunsan bai karyaba shi.          Haɗa kayan Solomon yay gaba ɗaya ya kai ɗakin ya ajiye. Ya juya zai fita Yoohan ya fito. Dakatawa yay ya gaidashi cike da girmamawa. Yoohan da kejin kansa sakayau kamar ba shiba ya amsa masa idanunsa nakan kayan da Solomon ɗin ya ajiye masa. sai dai baiyi maganaba sai shi Solomon ɗinne yay masa bayani.            Zama yay ya gyara jikinsa tsaf, ya buɗe kayan duka, na Solomon ƙananun kayane, nasu baba malam kuma shaddace ruwan zuma da akaima ɗinki mai ƙyau kuma dai-dai shi kamar an gwada. Tunda yake a rayuwarsa bai taɓa saka kaya makamanta hakaba. Duk da kuwa suma a nasu yare suna ɗinka shigensu amma shi bai taɓa sha'awar yin hakanba. A yau kam sai yaji sun birgesa har yay sha'awar sakawa. Haka ya warwaresu ya saka.       Baisan lokacin daya furta kalmar ‘Woow!’ ba a fili yana sake kallon kansa a mirrorn ɗakin. A haka manager da shima yay shiri tsaf a kayan da aka kawo masan ya shigo ya samesa. Sosai yake yaba ƙyawun da Yoohan yayi a kayan shima, sai ko Yoohan ɗin ke sanar masa shi bai taɓa sakawa ba sai yau. Hamza yayi mamaki sosai, duk da daga jiya zuwa yau ya fahimci su Yoohan sunada tsauri ko a cikin Christians ɗin ma, dan ya karanci yanda guards ɗinsa suka ringa gudanar da al'amiransu.        Sun fito falo Yoohan yaci abinci, bayan ya kammala babu jimawa sai ga Abba da Baba malam sun shigo. Su kansu bakinsu bai iyayin shiru ba sai da suka yaba ƙyawun da Yoohan yayi a kayan. Ya duƙar da kansa ƙasa saboda kwarjinin da suke masa yana godiya a garesu, musamman yanda suka sakashi yay barci jiya bayan kwanaki tara daya kwashe baiyi ba.      Cikin hikima ta masu ilimi baba malam ya nuna masa basune ba, UBANGIJI ne yay ikonsa, su nasu kawai roƙone cike da yaƙinin samu. Duk da Yoohan bawai ya fahimci maganar tasu bane sosai saiya gyaɗa kansa kawai. Sun ɗanyi hira kaɗan, duk da Yoohan dai bai saki jikiba sosai. Hamza ne ke biyema su baba malam ɗin, Solomon ma baya saka baki. Wannna ɗan zaman nasu ya saka Yoohan ɗin sake jinjina mutuncin mutanen da sanin darajar ɗan adam ɗinsu. Sai da su baba malam sukayi sallar la'asar sannan sukai musu rakkiya har airportda kansu suna sake roƙon Yoohan ɗin yazo musu bikin salla harma da Manager.      Yako amsa zaizo kodan yay gaisuwa da yaran orphanage. ________________       Guards ɗin Yoohan sun iske madam Chioma ashe bata gari tayi tafiya zuwa ƙauyensu mamarta babu lafiya, saƙon kuma ya risketa bayan wucewarsu kano babu jimawa. Dan haka ta wuce hardasu joy da Gebrail. Su Victoria ne kawai da ƴan aiki suma saboda makaranta ne.       Sun shiga da tsaraban cikin gida suka ajiye har boss ɗinsu ya iso. Aiko zuwa biyar na yamma sai ga kiran Solomon yace suje su ɗaukesu a airport.         Su Abraham sunyi murna sosai na dawowar yayansu, sunata kallon kayan jikinsa mamaki na cinsu. Sai dai sun kasa tambaya dan babu fuska. Shi kuma bayan yaji komai na ciwon kakar tasu sai ya shige sashensa yay kiran momy.      Sun tattauna sosai ya basu shawarar ɗakkota a taho da ita nan Abuja ya dubata, dan ashe dama tun jiyan suke neman layinsa amma bai shigaba. Bayan sun ajiye wayar sai yay kwanciyarsa. Wani barcinne ya sake ɗaukarsa mai nauyi yauma. Bai kuma farkaba sai gabannin asuba. Washe gari tun kusan goma na safe su Momy suka iso abuja, sun iske Yoohan ɗin ya gama shiryawa tsaf game da jikin kakar tasu. Suna isowa kuwa ya dukufa kanta. Cikin amincin UBANGIJI sai gashi tun aranar jikin nata ya fara sassautawa.         Wannan hidimar jinya ce ta mantar da madam Chioma sake bin ba'asin zuwan Yoohan kano har ma hutunsa ya ƙare yabar abujan. *_A KWAN A TASHI_*        Babu wahala wajen UBANGIJI, dan gashi yau saura kwana biyu kacal salla, kowanne yanki na musulmi suna cikin shirye-shiryen ta da yin bankwana da azumin watan ramadhan😢.       Yayinda su Nu'aymah ƴan saudia keta shirin dawowa suma a ranar sallar...........✍ _____________________ SAHFAT PREORDER! ______________________         Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗. SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya. Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske. *_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._* _To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_. Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU. Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa. *_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_* _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[5/17, 11:01 PM] Amina Mama: Alhmdllh, barkanku da salla. Barkanmu da dawowa filin daga. Da farko zan fara da baku haƙuri akan ɓacewata ɓat tun kafin azumi. Uzirine babba kuma mai ƙarfi da bazan iya ajiyesaba ya riskeni. Amma Alhmdllh komai ya daidaita. Na kuma gode sosai da haƙurin da kukaimin. Kufara da wannan kafin gobe idan ALLAH ya kaimu. *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biyaba ki haƙura domin ALLAH🙏🏻☺️_* No. 25 ...............“Hajjo nikam mizai hana tunda kince bayan salla da sati uku za'ai bikin su Hajarah mu bari sai lokacin bikin muzo ni da Adawiya? Abinda zaki duba abune bana kusa ba, kuma gashi mu duka karatu mukeyi, musamman ma ni da nake gab da kammalawa. Idan har nace zan ringa jeka ka dawo zan iya samun matsala wlhy”.          Hajjo da ke sauraren yah Abdallah ta jinjina kanta cike da nazarin maganganun sa, ta sauke numfashi da gyara zamanta saboda ƙafarta mai mata ciwo. “Gaskiya kam Abdullahi ka fimu gaskiya daga ni harsu ɗan malam, duk da nasan suma ɗin kansu, abinda yasa wannan tunanin baizo musu ba, saboda ba'a gama dai-daita maganar su Kubrah ɗin bane ba. Na kula kamar shi mai auren Hajarah keson kawo wani tsaiko akan batun shiyyasa suka jinkirta harni na koma. Amma yanzu inaga ka barni dasu, zanyi magana ta fahimta da ɗan malam insha ALLAH”.         “Nagode sosai Hajjo, ALLAH ya ƙara lafiya da tsahon rai mai amfani. Ki daɗe kiyi ƙarko hajjajun mu”.      Murmushi kawai hajjo tayi da shaƙiyancin jikan nata. Daga haka suka cigaba da firarsu har zuwa wani lokaci ya fice ya barta tana ƙarasa shiri, dan Nu'aymah nacan ta tare a massallaci tana ibadar ALLAH.            Cike da farin ciki Abdallah ya faɗa saman gadonsa yana murmushi, insha ALLAH indai su baba malam suka amince zuwan nasu ya koma sai bikin su Kubrah yanada yaƙinin samun cikar burinsa. Dan babban fatansa shine shirinsa akan mallakar Nu'aymah ya tafi dai-dai, shima ranar ɗaurin auren su Kubrah a ɗaura nasa da masoyiyarsa, farin cikin rayuwarsa.        Wayarsa ya jawo dake a gefensa, ya shiga ma'adanar hotunansa yana kallon hotunan da yaytama Aymah a wannan zuwan nasu batare da ita kanta tasan yana ɗaukarba. Ya jima yana kallon hotunan kafin barci yay awon gaba da shi a wajen             Barcin nasa bai kai mintuna ashirin da ɗaukarsa ba Adawiya ta shigo gidan ita da maman Aaida. Ganin ɗakinsa a buɗe ya sakata nufar can tana faɗima maman Aaida, “Aminiya zauna ina zuwa, naga kamar Yah Ab yana gida ma”.      Ɗan murmushi maman Aaida tayi da bata amsa cike da zolaya. “To adaibi a hankali azumi ake hajjaju”. Batare da Adawiya ta bata amsa ba ta shige tana dariya.           Hajjo da dariyarsu ta sakata farkawa da ga ɗan barcin daya figeta itama ta fito dan taji ba muryar Adawiya bace kawai. “Baƙuwa mukayi a gidan?”. Ta faɗa lokacin da take fitowa falon. Maman Aaida dake latsa waya ta ɗago idanunta ta sauke akan Hajjo. Sai kuma tace, “Barka da fitowa hajiya”.       Hajjo dake mata kallon sani tace, “Barka dai ƴar nan, gashi kuma kamar na sanki”.      Da sauri maman Aaida ta zaro idanu waje da mamaki, sai kuma ta tuna maganar hajiya datai mata gargaɗi tun farko akan zuwa gidan, amma yau tsabar taurin kai sai gashi ta biyo Adawiya data dinga mata daɗin baki..........       “To ko dai kamanni ne?” Hajjo ta katse mata tunani. Da sauri maman Aaida tace, “Eh gaskiya hajiya inaga hakane, dan ni ƴar nance”. Cike da nazarinta Hajjo tace, “Oh to ALLAH sarki, kinsan idon tsufa ƴar nan. To barka da zuwa, halan ke ƙawar Adawiya ce?”.       “Eh hajiya”. Maman Aaida ta bata amsa a ɗarare, dan tasha jinin jikinta da kallon ƙurulla da hajjon ke binta da shi...          Ɓangaren Adawiya kam tana shiga ɗakin Yah Ab sai ta iske yana barci, ga wayarsa ajiye saman ƙirjinsa kamar wanda ya rungume mace. Harta juya zata fita, sai kuma zuciyarta ta ƙwaɗauta mata wani abu daban. Dawowa tayi da baya a hankali ta ɗauka wayar, kasancewar ta jima da sanin password ɗinsa sai batasha wani wahalar buɗewa ba. Gabanta yay bala'in faɗuwa saboda cin karo da hoton Nu'aymah da tayi, ta kafe hoton da idanunta da suka ciko da ƙwalla, sai kuma ta kalli Abdallah dake barcinsa hankali a kwance batare da yasan tanai ba. Harararsa tayi kamar idanunta zasu faɗo, mikuma ta tuna oho mata, saita ajiye wayar a inda ta ɗauka ta fito a ɗakin.      Karo da taci da hajjo ta fito suna ɗan hira da maman Aaida yasata haɗiye damuwarta ta zauna tana gaisheta. WASHE GARI         Washe gari ya kama ranar salla, a kuma ranar Nu'aymah ta fito daga ittiqafi bayan sakkowa sallar idi. Duk da tayi ƴar rama sai gata ta ƙara haske saboda yanayin zafinsu da kuma zama cikin ac a koda yaushe. Tayi mamakin ganin Abdallah yazo ɗaukarta. Da farko taso taƙi binsa, amma ganin rana zatayi saboda yau zasu wuce sai ta haƙura ta bisa.       Motar tayi shiru babu mai magana a cikinsu har suka isa ƙofar gidansa. Tana ƙoƙarin buɗe ƙofar yay saurin saka lock. Juyowa tai tana kallonsa fuska a ɗaure, shima sai ya ɗaure tasan, batare da ya kalleta ba yace, “Inason muyi magana da ke a yau”.     Kamar bazata tanka masaba, sai kuma tace, “Yah Ab maganar mi? Dan ALLAH ka cire komai a ranka kamar yanda na cire nima, bana buƙatar wata sabuwar fitina dan girman ALLAH”.         Cikin zafin rai yace, “Saboda kin samu wanda ya fini? Nu'aymah minai miki ne a rayuwa har kika zaɓi sakamin da waɗanan abubuwan? Mina rasa irin na sauran maza ne.....?”       “Baka rasa komaiba Yah Ab, sai dai ka sani mu wannan itace ƙaddarar mu, UBANGIJI kuma shine yasan hikimar dake cikin yin hakan. ALLAH shine shaidata ban gujeka ba, ban kuma daina sonka ba. Sai dai wata katanga mai tsauri tariga da tayi gicci a tsakanin ƙaddarar mu. A ganina kuma babu amfanin maida yanda akayi domin bakin alƙalami ya riga da ya bushe.........”         “Sai dai idan kece kika busar da shi Nu'aymah, idan har kin amince inason a wannan karon mu cika burinmu na mallakar juna, na yadda da kaifin wuƙar data datse zaren ƙaddarar mu a wancan karon, sai dai a yanzu na sake ɗaura ɗammarar ɗaure zaren domin mu zama abu guda kamar yanda mukai fata”.      Murmushi mai ciwo Nu'aymah tayi, ta gyara zama tana fuskantar Yah Ab, cikin raunin murya tace, “Yah Ab, karka manta a yanzu kai ɗin mijin Adawiya da Yusrah ne, tayaya kake tunanin zan yarda ka sake ƙulle wancan zaren ƙaddarar da kaifin wuƙa ya datsa ta. A ganina muyi haƙuri kawai da yanda yau tazo garemu, domin kuwa jiyanmu ta wuce sai labari. Muyi haƙurin fuskantar gobenmu sai muzama masu cin riba. Wlhy Yah Ab bazan taɓa iya haɗa zaman kishi da Adawiya da Yusrah b.........”      Da sauri ya saka hannu ya rufe mata baki, cikin matuƙar ɓacin rai yace, “Hakan ya zamemiki dole kuwa Nu'aymah, idan kuma kikace zakimin taurin kai, wlhy a yanzu sai kunbar ƙasarnan da Adawiya tare da takardar sakinta ɗai-ɗai har uku kuwa”. Yana gama faɗar haka ya cire lock ɗin motar tare da ficewa a fusace.            Nu'aymah da tun farkon fara maganarsa akan su Adawiya ta ɗaura hannu a ƙirji da faɗin, “Na shiga uku ni Zainab! Yah Ab mi kake faɗi haka?”. Bai saurareta ba ya shige gida, da sauri itama ta buɗe motar ta fito ta bisa da ɗan gudu tamkar zata faɗi.           Adawiya dake a ƙwance bayan motar tai saurin cire hannunta data toshe baki, dan daƙyar tai control ɗin kanta lokacin da Abdallah ya furta zai sakesu inhar Nu'aymah bata amince da buƙatarsa ba. Motar ta buɗe ta fito itama da sauri tana faɗin, ‘Tabɗi jan, ashe lokacin yin yaƙin duniya na uku ya gabato kenan, lallai yanzune za'a fara wasan na gaske wlhy’. Ta ƙare maganar hawaye masu zafi na gangarowa a kumatunta.     Tun lokacin da taji Abdallah na sanarma Hajjo shine zaije ɗaukar Nu'aymah bayan an idar da sallar idi ta ƙudiri aniyar binsa a ɓoye. Dan haka kawai taji a ranta akwai manufa a zuwa ɗaukar, dan ta gama fahimtar take-taken Abdallah tun lokacin dasu Nu'aymah suka zo ƙasar. Shinefa ta lallaɓa taje ta shige motar ta ɓoye sannan ya samama hajjo inda zatayi sallar idi a massalacin, shi kuma batare dayin wani tunani ba yana zuwa yaja motar ya wuce. Kuma harya ɗakko Nu'aymah hankalinsa bai kai akan Adawiya dake lafe a ciki ba. wadda ko sallan idi ita batayi ba.         Tana shigowa cikin gidan duk a falo ta iskesu har Nu'  Abdallahn. Duk suka bita da kallon mamaki dan sunta nemanta bayan idar da salla basu gantaba, shine Ahmad yace suyi tahowarsu tunda ita ɗin ƴar garice ai.       “Ke kuma dama ba gidan kika dawo ba?”. Abdallah ya faɗa cikin kaushin murya dan har yanzu ransa a ɓace yake. Kamar bazata tanka masa ba, dan ranta a bala'in cinkushe yake, ji take kamar ta burmama Nu'aymah wuƙa ta mutu kowama ya huta. Amma komi ta tuna oho mata, sai tai kalar tausayi tana haɗiye ƙududun daya tokare mata maƙoshi. “Eh na biya nan maƙwafta wajen Umm-Farukh, dama wasu kayane mukai da ita zan amsarma su Aymah to kuma ma dai anyi rashin sa'a basu isoba, dama daga Mexico ake kawo matasu”.        Ɗauke kansa yay bai tanka ba, sai Ahmad ne da Hajjo sukai magana. Nu'aymah da tasha jinin jikinta akan yanda Adawiya ke magana ma bata tanka ba, sai dai a ƙasan ranta bata yarda da itaba sam. ★★★       Duk yanda Abdallah yaso sake keɓewa da Nu'aymah dan su sake cimma matsaya akan zancensu taƙi basa dama har suka wuce Nigeria bayan awanni huɗu da sakkowa idi, dan kobi takan bikin sallar da ƴan saudia ke gudanarwa basuyi ba, dama Adawiya ƙin dafa komai tai saboda takaici. Abdallah zaiyi magana kuma Hajjo ta hanashi, acewarta su da zasu tafi yanzu mizasuyi da wani abincin salla bayan nasu nacan na jiransu a ƙasarsu.                Sun sami ƙyaƙyƙyawar tarba kuwa daga su baba malam, dan ana sakkowa daga sallar juma'a (da yake ranar sallar ta kama juma'a ne) suka nufi airport domin tarbar mahaifiyarsu tamkar yanda suka saba. Babu kunya Nu'aymah taje ta rungume Baba malam, dan harga ALLAH tayi kewarsa shi da Umm da Muhammad. Kai dama ƴan gidan duka.      Fuskar baba malam ɗauke da murmushi ya shafa kan ƴar tasa yana faɗin, “Ja'ira, duk ga iyayenku cike da wuri bakiga kowaba sai ni ko?”. Fuskar Nu'aymah washeda murmushi tace, “Abba nayi kewarka ne sosai, kuma ALLAH kullum sai nayi mafarkinka kai da Ummuna”.      Baice da ita komaiba sai murmushi kawai daya sakeyi, dan shi mutum ne mai tsananin kawaici ga yaransa, yanama ƴan uwansa kara sosai. Dan haka suma a kullum suke ƙoƙarin koyi da ɗabi'unsa akan nasu ƴaƴan.           Bayan Nu'aymah ta ƙarasa ta gaida sauran iyayenta uku suma cike da girmamawa. Suma suka amsa mata da tsananin kulawa sai suka runguɗa gaban mahaifiyarsu suna jera mata sannu da zuwa. Cike da kulawa da kewa take dubansu, fuskarta faɗaɗe da murmushi. Ta kama hannun Abba Musbahu tana faɗin, “Wayyo autana duk ka faɗa, ko azuminne?”.      Dariya Nu'aymah da Ahmad sukayi, Malam ƙarami da Omar na tayasu kuwa. Hakama su baba malam sunata murmushin akan diramar autan nasu da mahaifiyarsu.             Lokacin da suka iso gidan nasu sun iskeshi da dangi da yaransu na ma'auri duk anzo tarbar hajjo da kuma yawon salla. Inda gidan ke wadace da tarin abinci kala-kala da kowanne sashe ya tanada. An gyarama hajjo sashenta tsaf an kuma kai mata abinci daga kowanne sashe an ajiye mata. (Dama haka suke mata).             Motocin na gama tsayawa Nu'aymah bata tsaya sauraren masu tarar tasu ba ta shige sashensu da gudu tana ƙwalama Umm kira. Da sauri Umm dake ƙoƙarin fitowa taja baya dan kaɗan ya rage suci karo da Nu'aymah.         Faɗawa jikinta tai ta ƙanƙameta tana faɗin, “Wayyo Ummuna, nayi kewarki wlhy”. Umm dake murmushi ta amshi ɗiyar tata da hannu biyu ta rungumeta itama, sai da ta tabbatar sunji ɗumin juna kowa na sauke ajiyar zuciya kafin ta ɗagota da ga jikin nata. “Nu'aymah! Yaushe ne zakiyi hankali kisan kin girma ne? Bakisan yanzu ba da bane, shekararki goma sha bakwai fa kina shirin shiga sha taƙwas”.      Cike da shagwaɓa ta saka kanta a kafaɗar Umm tana faɗin, “Umm ni indai ina gabanki wlhy jaririyace sabuwar haihuwa, nayi kewarki ne sanyin idaniyata. Ina Muhammad yake?”.           “Nayi cinikinsa” Umm ta bata amsa tana janyeta daga jikinta ta fice domin shiga tawagar masu tarbar surukar tasu.              Baki Nu'aymah ta tura gaba, ta ɗaga ƙafa zata biyo Umm tajiyo muryar Muhammad a bayanta yana faɗin, “Marhaban biki Aunty na”. Saurin juyowa tai garesa, sai kuma ta nufe da sauri kamar yanda yake nufota suka rungume juna cike da kewa da ɗoki.         Haka gidan ya kasance a hargitse ranar saboda shagalin bikin salla, Nu'aymah bataje ko inaba, dan bayan tayi salla taɗanci abinci sai ta shiga ta gaida kowa na gidan, kafin ta koma ɗakin Umm tai kwanciyarta, duk wanda yazo musu yawo a ranar bai samu ganinta ba, dan ta ɓoye kanta a cewarta saita huce gajiyarta da ƙyau tunda dai tasan zasu zaga gari yawon sallar gobe idan ALLAH ya kaimu ai. ___________            Kiran sallar la'asar ne ya tada Nu'aymah dake kwasar barcin gajiya. Ta miƙe da ƙyar dan jikinta ko ina ciwo yake faman mata. Wanka ta farayi, ta saka ɗaya daga cikin kayan sallarta. Tayi ƙyau sosai cikin shaddarta ruwan hoda, taji aikin stones da yay ƙyau sosai. Kayan sun mata ɗas ajiki, tare da sake fiddo haskenta saboda ƴar ramar da tayi.          Lokacin data fito Umm kanta sai da tace, “Masha ALLAH”. Hakama ƴaƴan yayun Umm ɗin su uku da sukazo mata yawon salla duk sai da suka yaba ƙyawun da Nu'aymahr tayi. Ta zauna fuskarta da murmushi tana gaidasu cike da girmamawa. Dan dukansu matan aurene, kuma duk suna da yaransu. Cike da kulawa suke amsa mata, kowanne na mata ƙorafin rashin zuminci, musamman babbarsu.        Nu'aymah tace, “Lah Aunty Zulfah wlhy ba rashin son zuminci bane, ni abinda yasa banason zuwa gidanki wannan ƙanin mijin naki takuramin yake wlhy. ya cika shegen kallo kamar ɗan daudu”.       Dariya suka sanya gaba ɗayansu, aunty Zulfah tace, “To kwantar da hankalinki, indai Fa'iz nema aurensa zaiyi, tunda ke kinƙi. Kinga nima dakin yarda ai dana samu ƴar uwata kusa dani ko.......”       Da sauri Nu'aymah ta katseta da faɗin, “Taf, aunty daina faɗa dan ALLAH, wlhy ya cika iyayi, banason namiji yayta gwalli kamar wani mace, shiba ɗan daudu ba shiba mata maza ba”.            “Amma Nu'aymah baki da kirki wlhy, kin gama ɗebema ƙanin mijin aunty Zulfah albarka gaba ɗaya”. Aunty Rafi'a ta ta faɗa tana dariya. Ita kanta Nu'aymah dariyar takeyi, Umm dai batace musu komaiba. duk da kuwa tana zaune tana jinsu.        Sai da suka tsagaita da dariyarne Nu'aymah ta miƙe tana faɗin, “Umm yunwa nakeji, ALLAH yasa akwai waina dai?”.          “Kin kuwa makaro, dan su Basira na ɗeboma ita gaba ɗaya, kinsan zakici wainar kikaƙi ɗiba ki ajiye?”. Kamar Nu'aymah zatai kuka tace, “Kai Umm! ALLAH yanzu kin daina sona, amma yanzu duk wainar dana gani ace ta ƙare? Su su aunty Basiran miyasa basu zauna sunci a sashen Addah b.......”        Harar da Umm take jefo matane ya sakata yin shiru, dan su Basiran ƙannen Adda ne. “ALLAH ya shiryeki to, to ance miki sune kaɗai suka cinye. Ga yayunki nan suma duk ita sukaci, sannan Abbanku da yay baƙo duk da baya a gidan shima ita yace akai musu kafin ya iso gidan”.          Komawa tai ta zauna kamar zatai kuka, su Aunty Zulfah nata tsokanarta wai ta amshema Muhammad guri tana shagwaɓa bayan shine auta.      Umm tasan yanda Nu'aymah keda jarabar son waina, dan haka ta dubeta sau ɗaya ta ɗauke kanta tana faɗin, “ki wuce sashen hajjo idan bata ƙareba”. Aiko zumbur ta miƙe, a ranta tana fatan ALLAH yasa ta samo.       Duk da takalman data gani na maza a ƙofar falon na hajjo kusan ƙafa biyar bata damu ba, sallama tayi kawai, kafimma su gama amsa mata ta shige dan duk zatonta yayunsune a ciki, tunda tasan duk suna gidan. A shagwaɓe ta buɗe baki zatai magana. sai dai cin karo da fuskar da batai zato ko tsammanin gani ba ta sata waro manyan fararen idanunta waje cike da al'ajabi.       Yoohan dake zaune shima cikin Suit ruwan babypink kallon nata yake cike da mamaki, a ransa faɗi yake, ‘Dama yarinyarnan ba'a cikin Orphanage ɗincan take ba? No wander ɗazun baiga komai kama da itaba a cikin yaran’. A fili kuwa sai ya ɗauke kansa cike da shan ƙamshi kamarma irin bai ganta ba ɗin nan shi.......         “Lafiya wai kika tsayama mutane ƙerere a kai Zainabu?”. Maganar Hajjo ta katse mata tunaninta. Juyawa tai inda hajjon take, har yanzu mamakin ganin Yoohan ɗin bai barta ba, “Hajjo wannan mutumin kuma ina kika sanshi?”.      “Wa ɗin?”. Cewar Hajjo tana kallon inda Hamza Manager, Yoohan dasu baba ƙarami ke zaune.         Maimakon Nu'aymah tai magana sai ta je ta zauna kusa da hajjon, matsar da bakinta tai dai-dai kunnen Hajjo tace, “Hajjo arne ne fa wlhy”. “Aina sani” Hajjo ta bata amsa cikin nuna halin ko in kula.      Sosai mamaki ya kume Nu'aymah, tai tsai tana kallon Hajjon, kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta sake maida dubanta ga Yoohan daya maida dukan hankalinsa kan wayarsa.        “Wai lafiyarki kuwa? Kina ganin mutane baki iya gaisuwa bane? Sai shegen kallo malama”. Yah Ahmad ya faɗa idonsa akan Nu'aymah. Sai da taɗan tura baki kafin ta duba Hamza manager data wuce da dukanin imaninsa tace, “Ina yini”. Cikin narkakkiyar murya da shi kansa baisan ta fitaba ya amsa mata da “Lafiya lau ƙanwarmu, kinyi salla lafiya?”. Kai ta gyaɗa masa kawai, dan duk sai taji kuma ta takura da kallon da yake mata. Ganin bata gaida Yoohan ba ya saka Malam ƙarami hararta, yace, “Shi kuma fa?”.        Yanzun kam baki ta kumbura sosai, ta kalli Yoohan ɗin da yay tamkar baisan da zaman kowaba a falon tace, “Good evening.           Sarai yajita, amma sai ya share baiko motsaba. Sai da Hamza ya ɗan taɓasa da faɗa masa ana gaishesa sannan ya ɗago manyan idanunsa farare tas ya sauke a cikin nata. Karan farko da sukaima juna kallon ido cikin ido. Kusan lokaci guda kowanne gabansa ya faɗi. Nu'aymah tai saurin fara janye nata da ƙoƙarin juyawa daga saitinsa.       Shima ɗan lumshe nasa yay ya buɗe (dan hakan ya zame masa kamar wata ɗabi'a) cikin muryarsa mai amo ɗin nan yace, “Kina lafiya?”.        A mugun razane Nu'aymah ta sake waigowa inda yake, har taune harshenta take wajen faɗin, “What?! Dama kanajin hausa?”.       Yanda tayi tambayar sai da ya saka su hajjo yin dariya. Hakan sai ya ƙarama Nu'aymah takaici, musamman ganin yanda Yoohan ɗin ya wani yamutse fuska, tare da miƙewa saboda wayarsa da aka kira, dama shi baiyi dariyarba. Sai da yazo daf da ita a hankali yace, “Yeyye girl”.        Kafin wani ya sake magana a cikinsu, ko ita ta bashi amsa Abban su Adawiya da Abban Musbahu suka shigo falon da sallama. Shi kuma ya fice yana amsa wayar.        Daurewa tai ta shiga gaishesu tana ɗan harar ƙofar da Yoohan yabi ya fice ta gefen ido, a ranta kuwa sai cewa take, ‘Oh ALLAH, amma dai gayen nan akwai munafurci, dama yanajin hausa amma duk sanda suka haɗu yake nuna mata bayaji, jibesa da wani shegen aski kamar kan zakara, sai kuwa yaga yeyye kafin yabar gidan nan yau’.       Duk kallon harar Yoohan da take Manager yana kallonta ne ta gefen ido shima, sai da Abban Musbahu ya kira sunansa ne sannan ya maida hankalinsa garesa, a ransa yana mamakin yanda alamu suka nuna akwai sanayya tsakanin Yoohan da wannan Zuƙeƙiyar budurwar data gama tafiya da dukkan imaninsa a kallo ɗaya.         Ita kam Nu'aymah da batasan yanayi ba sai ta lallaɓa ta fice dan jitai tama fasa cin wainar, yau duk yanda za'ai sai taji dalilin shigowar wannan kahirin cikin gidansu, harma falon kakarsu...........✍ 😜Kina ruwa Aymah😸. ______________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻. [5/18, 12:14 PM] Amina Mama: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*. No. 30 ................Lokacinda su Solomon ke acan cikin tashin hankalin tsoron cikar lokacin da papa ya basu akan sanin inda Yoohan yake, shi yana nan suna shirin tafiya massallacin juma'a shi da su baba malam.       Kowa ya kalli baba malam ɗin a yau zai fahimci yana cike da tsantsar farin ciki. A cikin nishaɗin daya shiga da shi cikin gidan nasa ya sake fitowa shi da Umm data taimaka masa yay shirin massallaci.     Ƴar tsokanar da ya kema Umm yasa Nu'aymah dake zaune a falon tana gyaran fruit ɗin da Umm ta sakata ɗagowa tana kallonsu. Cikin washe baki tace, “Abbah yau dai kana cikin farin ciki ALLAH, naga tun safe fuskarka sai annuri takeyi”.       Da ga Umm har baba malam dariya sukayi, ya matsa kusa da ita tare da kai hannu ya shafa kanta. “Tabbas yau ina cikin farin ciki mamana, saboda wannan farin cikin yau har ƙyauta ta musamman na shirya miki ke da Muhammad, dan haka kafin na dawo ki shirya faɗa mini abinda kike so”.          Sosai farin ciki ya sake kamata. Ta shiga jera masa godiya da addu'ar fatan dawowa lafiya. Daga shi har Umm amsa mata suke cike da kulawa. Kowannensu najinta a ransa sosai, dan daga Umm har Baba malam ba ƙaramin so sukema Nu'aymah ba. Suna dannewane kawai saboda ƙarfafama kansu tarbiyarta. Ga ɗunbin tausayinta dake mamaye da ruhinsu game da matsalarta. Dan har yau da muke ɗin nan baba malam bai gajiya ba wajen cigaba da neman likitan nan, yana kuma gayama UBANGIJI da neman taimakonsa a kowane daƙiƙa.      Bayan Umm tama baba malam rakkiya ta dawo. A inda tabar Nu'aymah nan ta sake isketa tana ƙalular gyara fruit ɗin.       “Nikam naga takaina da wannan hali naki Nu'aymah! Mutum yayta abu sanyi-sanyi tamkar bazai ƙaresa ba. Yanzu maimakon ki zauna kiyi aikin nan a kitchen shine kika taho nan kuma dan salon neman ɓata guri?”.        Baki ta tura gaba tana ɓata fuska, “Yoni Umm idanfa na zauna a kitchen wlhy Rabi damuna zatayi da surutun ta, kin sani dai ko redio haka ta ganta ta ƙyale akan zanc........”       Bammm!. Umm ta make mata baki, hakanne ya hanata ƙarasa faɗa. Da sauri ta saki wuƙar hannun nata hawaye na taruwa mata a ido. Umm dake hararta tace, “Saunawa zan faɗa miki karna sake jin wannan maganar banzan a bakinki Nu'aymah? Rabi bata girmeki ba? K wai yaushe ne zaki bar tsiwa da rashin kunya? Itaɗin sa'arki ce?”.        “Kiyi haƙuri Umm bazan sakeba ALLAH ”.       “Kima sake mana, mara wayau kawai”. Umm ta faɗa tana hararta da barin wajen. Harta kusa ƙofar sashen baba malam ta juyo. “Kiyi ki tashi a wajen nan kuma kafin na fito, ga man-shanu can a kitchen ki ɗauka ki kaima Addah, kuma idan kinje ki zauna shiririta karki dawo ki ƙarasa aikin dana sakaki kinji ko”.         Sake ɓata fuska Nu'aymah tayi hawaye na zirara mata. Sai dai batace komaiba har Umm ta shige ciki. Dan zuciyar gadon tazo mata wuya.              Duk yanda Umm tace tayi haka tayi, sai dai data shiga kitchen Rabi tasha harara, dan a ganinta saboda itane Umm ta Mammangare ta. oho ita batama san tanaiba, dan aikinta takeyi koda ta shigo bama ta kalli inda Nu'aymahn takeba tunda tasan basa doguwar magana lafiya sai sunyi faɗa.        Manshanun ta ɗauka zuwa sashen Addah. Sai da tai sallama kusan sau uku kafin a amsa mata ciki-ciki. Bata damuba ta shige tana ɗaure fuska dan har yanzu akwai haushin faɗan Umm tare da ita. Kubrah kawai ta iske zaune a falon, tunkan ta ƙaraso ciki take jefo mata harara.        Jitai kamar ta juya dan haushi, amma sai ta daure ta ƙarasa da faɗin, “Aunty Kubrah Umm ce ta aikoni wajen Addah?”.      Banza tai mata tamkar bata jitaba, har Nu'aymah ta fara yanke shawarar juyawa sai ga Hajarah ta fito daga ɗakinsu hannunta ɗauke da Al-qur'ani.        “A'a Aymah ce a wajen namu?”. Ajiyar zuciya Nu'aymah tayi da maida kallonta gareta. Fuskarta da ɗan damuwa tace, “Aunty Hajarah Umm ce ta aikoni wajen Addah. Amma ina tambayar Aunty Kubrah tamin banz.....”            Kafin ta ƙarasa taji saukar duka a bakinta, Kubrah da tai dukan ta nunata da yatsa cikin magana ƙasa-ƙasa tace, “K dan uwarki ni sa'arki ce ko?”.        “Kai haba Aunty Kubrah daga tambaya, yanzu dan ALLAH mita miki zaki dakar mata baki? Minene abin laifi anan to?”. Hajarah ce mai maganar dai-dai tana ƙarasowa inda suke ta kama hannun Nu'aymah dake hawaye, dama bakin bai gama mata zafiba akan dukan da Umm tai masa yanzu. Ga kuma Kubrah ta ƙara mata wani.     Cikin masifa Kubrah ta kalli Hajarah, “Kozaki rama mata ne?”.      “Bazan rama mata ba, amma ALLAH zai saka mata. Tunda duk wanda ya zalinci wani ALLAH na kallonsa. Nu'aymah jeki Addahn na ɗakinta kinji ko”.       Kai Nu'aymah ta ɗagama Hajarah tana share hawayenta. Batare datace komaiba ta nufi ɗakin Addah zuciyarta na mamakin yanda Aunty Kubrah kejin zafinta a ƴan kwanakin nan, duk da dai dama ita babu wani shaƙuwa sosai tsakaninta da ita tun da can. Sai dai bata taɓa nuna mata banzan hali irin na wannan karonba. Tana gab da shiga ta tsinkayo muryar Kubrah na faɗin, “Ƴar iskar yarinya ki taka a sannu dan a tafin hannuna kike wlhy, inba hakaba saina tona asirin iskancinki a gaban kowa yasani a gidan nan”.      Sosai gaban Nu'aymah yay bala'in faɗuwa, dan tasan inhar Kubrah ta faɗi abinda ta gani tsakaninta da Yoohan ranar tata ta ƙare. Da ƙyar ta iya haɗiye kukan daya taho mata.         Da mamaki Hajarah ta kalli Kubrah, “Haba Aunty Kubrah wace irin maganace haka? Wai nikam minene ya haɗaki da Nu'aymah mai zafi a kwanakin nan dan ALLAH?”.       “Ki shaƙeni in faɗa miki mana”. Kubrahn ta faɗa a harzuƙe.       “ALLAH ya baki haƙuri”. Hajarah ta faɗa tana barmata wajen ranta fal tunane-tunane kala-kala akan ƴar tsamar yayar tata da Nu'aymah data gaza fahimtar tushenta a kwanakin nan sam.        Sai da Nu'aymah tai sallama Addah ta bata izinin shiga sannan ta shiga ɗakin. Tsaye ta isketa tana ninke abin salla alamar sallar ta idar. Ganin Nu'aymah na sharar hawaye yasa fara'ar fuskar Addah gushewa lokaci guda. “Lafiya Nu'aymah? mi akai miki?”.        “Babu komai Addah, Umm ce tace na kawo miki wannan”.     Sam Addah bata yarda da maganar Nu'aymah ba, dan haka tai shiru tana cigaba da kallonta kawai batare data amshi man-shanun ba. “Nu'aymah bana son shirme, faɗamin gaskiya mi akai miki?”.       “Addah wlhy aunty Kubrah ce ta dakar mata baki dan hawai tacemin ta tambayeta kina ina ta mata banza”. Hajarah dake shigowa ɗakin ta bama Addah amsa.       Cikin ɓacin rai Addah tace, “Kubrah?!”.        “Eh wlhy Addah, ni bama dukan ya ɓatan rai ba, bakiji yanda take faɗama Nu'aymahr maganar banza ba. A kwanakin nan dama na kula tana matsama yarinyar nan a gidan nan, haka ɗazun a islamiyyar asuba dan kawai Nu'aymah ta fiddo Fahad ɗin maman Sadiya daga aji saboda suna faɗa da wani yaro wlhy bakiga abinda tai mataba. Alhalin baikamata taima Nu'aymahn maganaba tunda yaran duk ƴan ajintane, ta fita sanin halin kowa a cikinsu”.       Kama hannun Nu'aymah Addah tayi suka fito ranta a ɓace. Hakan yasa Hajarah biyo bayansu da sauri itama.          “Kubrah!!”. Addah ta ƙwala mata kira ganin bata a falon.     Da sauri ta fito daga kitchen hannunta ɗauke da plate ɗin abinci.      “Ubanmi Nu'aymah tai miki kika daketa?!”.         Sake tsuke fuska Kubrah tayi, ta kalli Nu'aymah data duƙar da kai tana hawaye har yanzun. Wani ɗan murmushin mugunta tayi kafin ta kalli Addahn. “Addah catai na daketa?”.        “Ni na faɗa ba ita ta faɗaba, tunda a gabana akai komai”. Hajarah ta bata amsa kafin Addah tai magana.       “Mtsooow!! Munafuka kawai. Addah ni ban daketa haka kawaiba, rashin kunya zataimin shiyyasa........”      “To amma shine zaki ce mata ƴar iska, kuma sirrinta a tafin hannunki yake. Idan kinso zaki tona mata asiri agaban kowa”.        “Wlhy Hajarah zan sauya miki kamanni, wai ni sa'ar wasanki ce?”.          “Kai!! Ya isheni haka, banason rashin mutunci. Bazan ɗauki wannan wawancinba kunji na faɗa muku. Shin kuɗin yaran goye ne da kullum baku da wani buri sai na samin ciwon kai? Kusani daga yau na sakejin makamancin wannan banzan al'amarin wlhy sainayi ƙololuwar ɓatama mutum rai a gidannan. Banda k kullum girma kike kinacin ƙasa Nu'aymah ce kuma ta zama abar tozartawarki Kubrah? To daga yau na ji wani abu ya sake fitowa makamancin wannan zakiyi nadama a gidannan kinji na faɗa miki”. Ta ƙare maganar da matuƙar zafin rai tana sake yima Kubrah gargaɗi da hannu.    Sai kuma ta juya ga Nu'aymah dake sauke ajiyar zuciya a jajjere. “Nu'aymah jeki wanke fuskarki kinji  kuma kar naji wannan maganar a wani waje, kiyi haƙuri”.      Kai Nu'aymah ta jinjinama Addah, babu musu ta shiga toilet ɗin dake a falon ta wanke fuskarta ta fito. sallma tai musu ta fice batare data sake yarda ta kalli sashin da Kubrah take ba. Harga ALLAH hankalinta a tashe yake matuƙa da kalaman Kubrah.            Koda ta koma sashensu ɗakinta ta shige ta shiga raira kuka, Nu'aymah yarinyace da bata da tsoro sam. Amma yanda tai matuƙar damuwa da faruwar abin nan na jiya daya kasa barin ransta saita baka tausayi. Tasan tabbas wannan laifin na jiya yasha banban da kowane irin laifi, kuma duk wanda zaiji abinda ya farun sai yayi ALLAH wadai da ita, ƙilama baba Malam da Umm su tsine mata albarka.      Sake rushewa tai da kuka kamar zata shiɗe wajen jan zuciya. A haka ta tsinkayo muryar Umm na ƙwala mata kira. Da sauri ta miƙe ta shiga share hawayen, harta nufi ƙofar fita sai kuma tai saurin dawowa. Toilet ta shiga ta sake wanke fuska tazo gaban mirror tasa hoda da kwalli sannan ta fita.          Zaune ta iske baba malam da Umm a falo. Cikin raunin murya taima baba malam sannu da dawowa. Duk kallonta sukai shi da Umm, baba malam yace, “Lafiya kuwa? Naga idonki kamar wadda tai kuka? Mamana!”.     Kafin tayi magana Umm dake hararta tace, “Saboda namata faɗa akan rashin kunyar data iya”. (dan ita tazata faɗan datai matane ya sakata fushi har yanzun).       Baba malam baice komaiba sai maida kansa da yay ga tv kawai. Fuska a ɗaure Umm ta nuna mata trayn dake a kan centre table. “Ki ɗauka ki kaima baƙo a falon baba”.      Kai kawai ta jinjina mata ta koma ɗakinta ta ɗakko hijjab. Batare datai maganaba ta ɗauka tiren ta fice. Sai da ta fice gaba ɗaya sannan baba malam ya ɗauke kansa daga kallonta. maidawa yayi ga Umm da itama take kallon nata.        “Addu'a ya kamata ki cigaba da mata bawai nuna fushinki da zafi fiye da kima ba. Har yanzu Nu'aymah yariyace ƙarama, sannan kinsan lalurar dake tare da ita sam bata buƙatar yawan takura. Ki fahimci ita wannan tsiwar itace tata ƙuruciyar”.         “Amma Malam ka tunafa ƴa mace ce ita. Gidan wani fa zataje. Bandama ƙaddara daba yanzu tana ɗakin miji ba. Wlhy sam bana son tsiwarnan tata, bansan a ina ta kwaso wannan banzan halinba nikam”.      Murmushi baba malam yayi yana miƙewa, “To ayi haƙuri zata daina insha ALLAH, nima zan zauna da ita anjima ALLAH ya huci zuciyarki”.        Yanda yay maganarne ya saka Umm yin murmushi, dan ta sake tabbatarwa yau mijin nata yana cike da nishaɗi sosai kam, musamman data san yafi kowa ƙin jinin tsiwar ɗiyar tasu. ★★★★★★              Murya a sanyaye tai sallama a ƙofar falon har kusan sau uku. jin shiru ba'a amsaba ya sakata tura kanta ciki da haushi. Takaicin rashin amsa mata sallamar da ba'ayiba ne ya sakata ƙin kallon baƙon ma balle tasan wanene.       A gabansa ta dangwarar da trayn, murya a cinkushe batare data kallesa ba tace, “Ina yini”.        Shiru yanzuma ba'a amsaba, wani sabon takaicin ya sake lulluɓe ta. Har tayi niyyar dubansa ta sauke masa takaicinta saita tuna yanzufa Umm ta gama mata faɗa harda duka akan tsiwa, sannan kuma bai kamatama tayi wani abun rashin hankali ba tunda batasan wanene baƙon nasu ba. Zata iya yuwuwa babban mutumne sa'an baba malam ko cikin yayunta. Haɗiye haushinta tai ta nufi hanyar fita zata bar falon.           Yoohan da tun shigowarta idonsa nakan wani littafi da baba malam ya bashi ya duba ya ɗan ɗago kansa dan sam baiji sallamarta ba balle shigowartaba ma shi, sai gilmawarta kawai ya gani yanzu da take ƙoƙarin fita. Cikin tsautsayi ta bigi ƙaramar jakkar dake gefensa da ƙafa. baya tai taga-taga zata faɗi cikin sa'a yay saurin saka mata ƙafa dan son kareta bisa tsautsayi sai gata a cinyarsa ɗare-ɗare.      Duk da ya canja kayan jikinsa mayataccen ƙamshin turarensa na nan manne da shi. Shaƙa ɗaya Nu'aymah tayi tai azamar ɗagowa cikin tashin hankali da tsantsar takaici.        Idanunsu ne ya shige cikin na juna, cike da firgici Nu'aymah ta sake waro masa idanunta da kware baki zatai ihu saboda harga ALLAH ta tsorata da ganinsa.  Saurin saka tattausan hannunsa yay ya rufe mata bakin ruf yau ma, tare da sake manneta a jikinsa sosai shima a cikin ɗan firgice.         Wani irin mugun bugawa ƙirjinta ya sakeyi, jikinta ya hau ɓari tamkar wadda aka jefa cikin garwashin wuta ko akan wayar lantarki. Ta shiga mutsu-mutsun ƙwace kanta tana kai masa duka.           “Oh my God! Just relax. Please calm dawn”. Ya faɗa yana janye hannayensa duka daga jikinta.        Cikin rawar jiki hawaye na zirara ta miƙe, sake bigewa tai da kujera ƙafarta ta tuzguɗe ta sake yin gaba kuma zata kifa yay azamar riƙo mata hannu ta sake dawowa jikin nasa.       “Wayyo Abbana ɗan isk.........” ta wage baki da iya ƙarfinta zata faɗa yay azamar saka hannu ya sake toshe bakinta da manneta sosai a jikinsa yanda bazata iya ko motsawa ba.         “Wa'iyazubillah!! Iskancin naku da rashin tsoron ALLAH yau har a falon malam?” Kubrah data shigo falon tamkar an jehota ta faɗa hannu bisa kai tana mai waro idanu waje..              Tashin hankali, tsabar ruɗewa Nu'aymah harda guntun fitsar ta saki a wando, batama san ta saka gwiwar hannunta ba ta kai ma Yoohan duka. Sai ko ya sauka a gefen cikinsa.       Saurin sakinta yay yana faɗin “Ouch!!!” dan harga ALLAH yaji zafi. Yay saurin ɗoura hannun nasa bisa cikin ya riƙe yana watsa mata mayun idanunsa masu haske da cikar gashi.        Nu'aymah dake ja da baya tana hawaye da kallonsa da kallon inda Kubrah take tsaye tace, “Ɗan iska kawai, ALLAH ya isa ban yafeba. Wlhy daga yau ka sake ƙoƙarin taɓamin koda hannu sai na illata maka wannan fuskar taka mai kama da jan ƙosai, na tsane ka wl........”         “Hhhhhhh! K! Ƴar iska bar wani pretending kinji!”. Kubrah ta faɗa tana ƙarasa shigowa cikin falon sosai.       Nu'aymah dake kuka tamkar ranta zai fita tace, “Aunty Kubrah wlhy ba abinda kike tunani bane. Wlhy tallahi kinji na rantse by mistake ne hakan ya sake faruwa yau ma, shine fa y.....”         “K dalla saurara mani! Mahaukaciya kika maidani irinki komi? Na ganki da idona saman cinyarsa kuna tsotsar bakin juna sannan ki hau mini wani rsantse-rantsen banza. Kinsan ALLAH, inhar kika sake faɗin tak saina kwarara ihu yanzun nan kowa yasan halin da kuke ciki”.      Ƙasa Nu'aymah ta durƙushe tana ƙara sakin kuka maiban tausayi. Yayin da Yoohan da sam bai fahimci mi Kubrah ke faɗa ba ya zuba musu idanu kawai yana kallonsu.      Juyowa Kubrah tayi garesa, sai dai wani shegen kwarjini da cikar haibarsa tai bala'in cika mata idanu. Muƙut ta haɗiye maganar tata ƙirjinta na wani irin bugawa da sauri-sauri. Cikin suɓutar baki ta firta ‘Tsarki ya tabbata ga ALLAH’.          Sake ɗaure fuska Yoohan yayi fiye da da, dan a rayuwarsa ya mugu-mugun tsanar kallo, musamman ma irin wanda Kubrah ke masa na ƙurulla a yanzun. Duk da ma bawai yaji mi take faɗaba ne ɗazun, sai dai ya fahimci ba magana mai daɗi takema Nu'aymah ba. Dan haka ya watsa mata wani mugun kallon da manyan idanunsa yana miƙewa.      Ganin ya nufita ya sata saurin zabura tai baya, sai dai kuma a mamakinta yama ɗauke kai daga gareta gaba ɗaya, raɓata yay ya nufi Nu'aymah dake durƙushe har yanzu tana kukan tashin hankalin datasan a yau babu makawa sai Kubrah ta tona mata asiri.         Handkherchief ya ciro a aljihunsa tare da tsugunawa gabanta, murya ƙasa-ƙasa yace, “Hello!”.       A razane Nu'aymah da batasan da isowar tasaba ta ɗago danjin maganarsa gab da ita. Ta waro idanu waje sosai da saurin duban inda Kubrah ke tsaye tana kallonsu kamar ta samu television.        Kamo hannunta yay, da sauri ta dawo da dubanta garesa tare da fisgewa da ƙarfi. Sai dai ko gezau baiyiba balle tai tunanin ƙwacewar. “Kai wane irin......”          Yatsansa ɗaya ya ɗaura akan baki. “Shiiii!!!” ya faɗa cikin katseta da zazzaro mata idanunsa sosai.          Ruf. Tai saurin rufe bakin kuwa. Dan wani irin shakkarsa da tsoronsa da bata taɓa fuskantaba daga gareshine ya shigeta yau ɗin. Ga wani irin kwarjini mai bala'in cika idanu da yay mata. Batare da yayi magana ba ya saka mata handkherchief ɗin cikin tafin hannunta tare da matso da fuskarsa gab da tata cikin wata irin raunanniyar murya yace, “Silly girl”.        Baya taja jikinta, dai-dai da sakar mata hannu da yayi ya miƙe shima. Batare da ya kalli ko inda Kubrah take ba ya ɗauka jikkar da Nu'aymah tai tuntuɓe ya fice abinsa. Ya tabbata idan ya cigaba da zama a falon to lallai zai iya aikata abinda shi kansa bazai yafema kansaba. Dan duk da baiji mi Kubrah ta faɗaba ya fahimci ba abune mai daɗi ba musamman yanda Aymah take kuka.           Yana ficewa Kubrah ta bi bayansa da sauri.       “Aunty Kubrah!” Nu'aymah ta faɗa da hanzari tana miƙewar itama. Amma sam Kubrah batako jiyoba balle ta nuna zata saurareta ta ficewarta.              اَللَّهُمَّ لاَ سَهْلَ إِلاَّ مَا جَعَلْتَهُ سَهْلاً وَأَنْتَ تَجْعَلُ الْحَزْنَ إِذَا شِئْتَ سَهْلاً. Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahlan, wa anta taj'alu-l-hzana idha shi'ta sahlan. Ya Allah! Babu wani abu mai sauki sai abin da Ka sanya shi ya zama mai sauki, kuma Kai kana sanya tsanani idan Ka so ya zama sauki.          Nu'aymah dake jin wata hajijiya na neman zubar da ita ƙasa ta faɗa tana mai dafe kanta da sauri. Da ƙyar ta iya kai hannu domin lalubar bango. Sai dai kuma ina bai kai ga bangonba wani duhu ya mamaye idanunta. a take ta zube ƙasa jikinta na karkarwa saboda wani bala'in sara mata da kanta yayi lokaci ɗaya..............✍ ZAFAFA BIYAR 2021 Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻. [5/18, 12:14 PM] Amina Mama: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta_*. No. 26 ..............Cike da jin haushin Yoohan Nu'aymah ta fito daga sashen hajjo. Hakan yayi dai-dai da shikuma Yoohan ɗin zai koma dan ya kammala wayar.          Karo sukayi, goshin Nu'aymah ya bugu da sarƙar Cross ɗinsa. Da sauri tai baya saboda azaba. Shima bayan yaja kaɗan yana wani yamutsa fuska idonsa a kanta. Kasancewar Nu'aymah bata taka ɗan step ɗin ƙofar falon hajjon dai-dai ba lokacin da tai baya sai ta sake yo gaba zata faɗi.            Yoohan ya tabbatar idan ya barta ta faɗi zataji mugun ciwo ne, dan haka da saurinsa kuwa ya tarota ta faɗo jikinsa. Sai kuma ta firgice saboda tsoratar da tai najinta kwance a ƙirjinsa, ta wage baki zata tsala ihu yay azamar ɗora lallausan tafin hannunsa saman bakin nata ya rufe ruf.          Cikin tashin hankali Nu'aymah ta fara mutsu-mutsun kwatar kanta, jikinta sai rawa ya ke yi. Shikuma yaƙi sakinta dan ya tabbatar yana sakin nata faɗuwar daya gudar mata a farko sai tayi wadda ta fita a yanzu, cike dajin haushi ya daka mata tsawa, dan jiyayma kamar ya saketa ta faɗin ma yaga ƙarshen rashin kunya.           Duk da tsawan da yay mata bata nutsuba, sai ma cigaba dayin mutsu-mutsunta nason ƙwacewa takeyi, tuni hawaye kuwa sun fara bimata kumatu, dan a rayuwarta da hankalin kanta kuma hakan bai taɓa faruwa da itaba. Ko hannu bata yarda samarin gidansu wani ya riƙe mata balle akai ga runguma irin haka. Sai gata yau kwance a ƙirjin ƙaton kahiri, da ko yayunta basu taɓa aikata haka a gareta ba. gashi ya rufe mata baki babu damar magana. Kuma ƙarfi ba ɗaya ba.........        Jin ya manneta da bango sai tashin hankalinta ya ƙaru, dan ta zata wani abun kuma zai aikata mata, ta kasa nutsuwa ta fahimci taimakonta yayi. hannayenta duka biyu ta saka tare da dukan ƙarfinta tana ƙoƙarin ture masa hannunsa daya rufe mata baki da shi. Ko gezau baiyiba, saima wani shegen kallo da yake binta da shi tamkar ya manta a inda suke, ga fuskarsa a matuƙar ɗaure balle kai tunanin da biyu yay hakan, sai dai shima zuciyarsa wani irin harbawa take da sauri-sauri.       “Ouch!!” ya faɗa da sauri yana janye hannunsa da ya toshe mata baki da shi, dan kuwa daddagewa tayi ta gasa masa cizo a tafin hannun. Yaja da baya yana yarfe hannun nasa da faɗin, “Are you mad?!”.        Nu'aymah da har yanzu jikinta bai bar rawa ba ta galla masa harara tana share hawayenta. “Eh banda shi. ALLAH ya isana kuma, wlhy ka sake gigin taɓani saina fasa maka kai, danni ba ƴar iska baceba!”.       “Silly girl! Waye ɗan iskan?” ya faɗa da turanci kamar yanda ta faɗa itama yana galla mata harara tare da cafkota, iya ƙarfinsa ya fisgota tayo baya ta sake faɗawa jikinsa. Mannata jikin bangon ya sakeyi, ya toshe mata baki da ɗayan hannunsa. kafin ya ɗago ɗayan hannun ya kalli inda ta cije sa, yamutse fuska yay ganin yanda shatin haƙoranta suka fito masa, ba wajen data ciza ɗin kawaiba, tafin hannun gaba ɗaya yayi jaa abinka da ba'asan wahala ba...        Nu'aymah ta rikice iyakar rikicewa yanzun kam, dan ta yarda a ranta da gaske Yoohan son cutar da ita yake. Ƙilama abinda ya kawosa gidan kenan. Sake kaima ɗayan hannun cizo tayi. Yayi saurin janyewa ya maye gurbin hannun nasa da bakinsa. Shi kansa baisan yaya akai hakan ta faru ba, ya tsinci kansa ne kawai da haɗe bakin nasa da nata ya shiga kissing ɗinta.        Yanda take kuka da turesa da yakushinsa ne ya sashi janyewa daga gareta da sauri. Duk da halin daya ganta na ƙololuwar shiga ruɗani da tashin hankali hakan bai hanashi kallonta ba, tare da zazzaro mata manyan idanunsa da suka sauya kala zuwa ja.       Harga ALLAH Nu'aymah ta tsorata yau kam, dan ta tabbatar tunda har ya iya mata wannan abun a cikin gidansu to lallai zai mata duk abinda yazo masa rai. Tunda tasan su basu ɗauki keta mutuncin mace a komai ba. Amma tsabar ƙarfin hali irin na mutuniyar taku ana sakar mata baki sai ko ta murguɗa masa bakin da sake zuba masa harara. iya ƙarfinta ta turashi dan har yanzun yana manne da ita ne a bangon, amma ko gezau baiyiba balle tasa ran samun hanyar kuɓuta. Waige-waige take gudun kar wani ya fito ya gansu a haka, tana kuma hawaye, cike da tsiwa cikin harshen turancin data san yafi fahimta sosai tace,         *_“Dama ku babu abinda kuka iya sai son taɓa mata da ɓata musu rayuwa, ALLAH ya isana ɗan iska kawai. shiyyasa wanda baya salla an haramta ma sa jin daɗin duniya. Sannan zai gamu da wahalhalu a wurare guda huɗu: A nan duniya, da ranar mutuwa, da cikin ƙabari da ranar hisabi. A duniya ana ɗebe ma sa albarka, a cire ma sa kwarjini daga fuska, a sa ma jama'a ƙyamar sa. A ranar mutuwa zai mutu da wulaƙanci da yunwa da ƙishirwa. A cikin kabari ALLAH zai ƙuntata ma sa, a hura ma sa wuta a cikin sa, a aika ma sa kumurci a tsakanin fatar jikinsa da namansa. A ranar hisabi za a baƙanta fuskarsa, a yi masa hisabi dalla-dalla, sannan a haɗa shi da zabaniyawa da za su wurga shi cikin wuta. Lallai, sallah ita ce ginshiƙin addini. Idan kaƙi gaskiya zaka faɗa ɓata. Idan ba ka ji nasiha ba, zaka yi da-na-sani. Wanda baiji bari ba ya ji hoho!......”_*      Ta ƙare maganar da sake turashi da ƙarfi. Yanzun kam da kansa ma ya matsa ya bata hanya, da gudu tabar wajen kuwa tana kukanta har yanzun.          Cike da takaicin kansa ya rumtse idanusa da ƙarfi, tare da ɗora hannunsa a goshi yana murzawa da abaton “Oh lord!, mina aikata?!”. ★★★★          A wani ɗan lungun sashensu Nu'aymah ta maƙale tana sauke tagwayen shashshekar kuka, har zuwa yanzu jikinta baibar rawa ba, sai faman waige-waige take tamjar ance mata Yoohan ɗin biyota yayi.        Ta ƙanƙame jikinta lokacin da abinda ya farun ya sake dawo mata a rai, yanda gashin jikinta ke wani mimmiƙewa zai tabbatar maka da tsigar jikinta tashi takeyi.      Da sauri ta saka hannu tana share hawayenta saboda jin tahowar mutum. ‘Na shiga uku ya biyo ni’ ta faɗa a fili zuciyarta na wani irin zallo tamkar zata faso ƙirjinta ta fito........        “Nu'aymah lafiya na ganki anan? Mi kikeyi ne haka?”.       Duk da ganin Aunty Kubrah ce ba Yoohan ɗinba hakan bai hana Nu'aymah sake rikicewa ba, ta shiga inda-inda jikinta na tsuma. “A..Aunty babu ko.. Komai”.        Kubrah data kafeta da ido taɗan murmusa, sai kuma ta juya bayanta tana faɗin, “Ki kwantar da hankalinki ai ba biyoki yayi ba, na tabbatar kuma babu wanda ya ganku a gidan nan”.         Wani muguwar faɗuwa gaban Nu'aymah ya sakeyi daboda jin furicin Aunty Kubrah. Cikin rawar harshe Nu'aymah tace, “Aunty Kubrah wlhy ni.......”        “Kinga kwantar da hankalinki Nu'aymah babu maiji, indai nice ko Hajarah baza taji wannan zancenba balle wani a gidan nan. Amma inason ki faɗamin gaskiya, yaushe kuka fara wannan abun ke da shi?”.        “Innalillahi! Aunty wlhy bamu taɓa yiba, yau ma na rantse shin......”        “Kinga ya isa. Share waɗan nan hawayen idan baso kike ki tonama kanki asiri ba da kanki”.        Nu'aymah duk ta sake rikicewa, tama rasa fahimtar inda maganganun Aunty Kubrah suka dosa saboda tashin hankali. Duk da ta share hawayen sun gaza tsayawa. Hannunta Kubrah ta kama har lokacin fuskarta da murmushin da Nu'aymah ta gaza fahimtar na minene. “Kinga muje sashenmu, idan ba hakaba Umm sai ta fahimci abinda ya faru, ko kinfi buƙatar hakan?”.      Da sauri Nu'aymah ta shiga girgiza mata kai, “A'a wlhy Aunty, banason Umm ta sani dan zata kasheni, dan ALLAH karki faɗa mata, wlhy kuskurene ba kuma laifina bane ba, na rantse da ALLAH Aunty ban taɓa yiba, ko hannuna Namiji bai taɓa riƙewa ba”. Ta ƙare maganar da rushewa da wani irin kuka maiban tausayi.      Komai Kubrah bata sake cewaba ta kama hannun Nu'aymah suka nufi sashensu. Ta ƙofar baya tabi da ita, dan ƙannen Addah su Aunty Basira suna falo zaune dasu Addah suna hira. Batare data bari sun gansu ba ta shige da Nu'aymah bedroom ɗinsu. Zaunar da ita tayi sannan itama ta zauna a kusa da ita. Har lokacin kuma Nu'aymah kuka takeyi, zuciyarta na ƙarajin tsanar Yoohan matuƙa........          “Ko shine Ameer ɗin Saurayinki?”.      Da sauri Nu'aymah ta ɗago tana kallon Kubrah, sai kuma ta shiga girgiza mata kai, “Aunty dan ALLAH ki yarda dani, wlhy Ameer ba saurayina bane. Wannan kuma bama musulmi bane ba, baƙone yau na fara ganinsa”.         Haɗe fusaka Kubrah tayi tamau tana kallon Nu'aymah ɗin. “Karkimin ƙarya Nu'aymah, inba hakaba wlhy na fasa rufa miki asirin, a yau da daddare zan sanarma Hajjo da Baba malam da Umm komai. Ki faɗamin tun yaushe kuke tare? Sau nawa kuma yay amfani da ke?”.        Duk sai Nu'aymah ta sake daburcewa, dan tama rasa wace amsa zata bama Aunty Kubrah, gaba ɗaya ta kasa fahimtar manufar Kubrah.......      Kamar Kubrah tasan tunanun da Nu'aymahn keyi, sai ta sassauta fuskarta tana gyara zama. Ta ɗan rage kaushin muryarta kuma ta koma magana cikin lallashi. “Nu'aymah kinsan dai yaya nake a gareki, duk abinda zan iya gani gasu Hajarah raina ya ɓaci idan nagani daga gareki dolene naji zafi, ɗiyar ƴar uwar mahaifiyata ce kuma ke, dan kuwa Umm tamkar ƴar uwar Adda take, tamafi min wasu ƴan uwan Addan. Yanzu Nu'aymah da wani ya ganki a gidannan ƙaton banza yana lalubeki mikike tunanin zai faru?, idan ma iskancin zakiyi ai gara kuyisa can a waje wani bai gankiba ko, amma a cikin gidanku? Babban gida mai daraja irin wannan? Wane kallo kikeson aima iyayenki maza damu kanmu Nu'aymah?”.           “Dan ALLAH kiyi haƙuri Aunty Kubrah, wlhy bazan sakeba wannan ma ƙaddara ce da kuma kuskure”.       “ALLAH yasa hakane to”. Kubrah ta faɗa tana wani ɗauke fuska da ƙyaɓe baki.              Nu'aymah na kuka tace, “Wlhy da gaske nake Aunty. Dan ALLAH ki yarda dani”.          “Nu'aymah idan ban yarda da ke ba minene amfanin musawar to?, tunda idan kunbar gabanmu ALLAH kaɗai yasan mi kuke aikatawa, masu iya magana fa kance rana dubu ta barawo, ɗaya tak ta mai kaya. Yau ɗinma ai bakiyi tunanin zan ganku ba”.           Ƙasa Nu'aymah ta zube tana kuka tamkar ranta zai fita, ‘Ita mizata faɗama Aunty Kubrah ta fahimceta ne wai? Wane rantsuwa zatai mata danta yarda ba da yardarta kafirin nan ya aikata hakanba a gareta?’.        Sai da taci kuka sosai, Kubrah na zaune na kallonta kafin ta ɗagota ta rungumeta, “Kukan ya isa haka, aina yarda ba laifinki bane. Na miki hakane kawai dan kisan baki dai-dai ba”.          “Na gode da kika fahimceni Aunty, kuma namiki alƙawarin hakan bazata sake faruwa ba insha ALLAHU”.      Ɗagota Kubrah tayi ta share mata hawayen tana murmushi, “Shikenan naji, kuma na miki alƙawarin babu maijin zancen nan a gidan nan kinji, kije bayi ki wanke fuskarki kizo ki sake shafa hoda dan karma wani ya zargi wani abun kuma kinji ko. Ki kuma saki jikinki inba hakaba Umm zata gane, kuma kinsan halinta. Zatabi duk hanyar data dace dan tasan gaskiyar abinda ya sakaki kukan”.            “Insha ALLAHU bazan bari ta gane ba Aunty, bara ma na wanke”. Ta ƙare maganar tana miƙewa da sauri ta nufi bayin su dake cikin ɗakin. Tana wanke fuska tana kallon bakinta a mirror. Wasu hawayen sai sake ƙoƙarin zubowa suke tana dannesu da ƙyar. A fili tace, ‘Na tsaneka mugu ɗan iska mai suffar samudawa, bazan taɓa yafe makaba wlhy”. Ta ƙare maganar da fashewa da kuka.      Taja kusan mintuna biyu tana kukan kafin ta wanke fuskar ta fito. Fitowar tata tayi dai-dai da shigowar Hajarah da wayar Kubrah a hannu. Da mamaki Hajarah take kallon Nu'aymahn, dan ita dai bataga shigowarta sashen ba.        “Nu'aymah yaushe kika shigo ne? Gashi kamar kinyi kuka?”. Da sauri Nu'aymah ta girgiza mata kai, sai kuma ta kalli Inda tabar Aunty Kubrah dan tana zaune a wajen, tana jinsu kuma amma ko kallonsu taƙi tayi balle ta nuna alamar tasan mi sukeyi ma. “Babu komai Aunty Hajarah, kaina ne kawai ke ɗan ciwo”.       Ƙarasawa inda Nu'aymahn take Hajarahn tayi, ta ɗago fuskarta cike da nazari........        “Wai miye hakane? Tace miki babu komai kanta ke mata ciwo miye na damunta ne kuma?”.        Baya Hajarahn taja kanta a ƙasa tace, “Kiyi haƙuri Aunty Kubrah, ga wayarki dama Alhaji ne ya kiraki”. Ta matsa inda take cike da girmamawa ta bata wayar.       Tana amsa ta nuna mata ƙofa da ido. Da sauri kuwa Hajarahn ta fice.      Kubrah ta maida dubanta ga Nu'aymah dake a tsaye har yanzu. “K kuma ki bada himmar tonama kanki asiri kinji ko, ki wuce ki shafa hodan, idan kuma sokike wani ya sake shigowa to”.         Gaban Mirror Nu'aymah ta ƙarasa. Ta shafa mai da hoda harda kwalli, duk da dai hakan fuskar dai babu walwala.      Amma sai Kubrah batace mata komaiba suka fito falo inda su Hajarah ke hira tare. Zama tayi kamar yanda Addah dake kallonta ta Umarceta. Su Aunty Basira nata tsokanarta da faɗin ina tsarabarsu ne?.        Tun tana noƙewa dai harta ɗan ringa amsasu, amma ta gaza sakin jikinta yanda ya kamata sosai. Duk motsinta Hajarah da Addah na lura da shi, sai dai babu wanda ya iya cewa komai a cikinsu.       ___________________________               A ɓangaren Yoohan kuwa duk yanda su Hajjo sukaso ya zauna jiran dawowar baba malam ya gaza hakan. Yace musu zai dawo da safe yanzu yanada wani uziri.       Badan hajjo taso ba ta barshi. har ƙofar gida su Yah Ahmad sukai masu rakiyya shi da Manager. Inda su Solomon ke jiransa a mota. Kasancewar basu iske baba malam ba yasa bai shiga dasu cikiba. Yace su jirashi a waje. Dan da ƙyarma Su Ahmad suka lallaɓashi ya shiga cikin gidan. Da farko ya ce zai koma tunda baba malam ya fita. Dan dama yaso yin surprise ɗinsa ne shiyyasa bai sanar masa shigowarsa kanon ba ma.          Har drivern sa ya tada mota ya tsaidashi. Kuɗi ya ciro a cikin jakarsa rafa guda na ɗari biyar sabbi ƙal ya miƙama malam ƙarami yana faɗin, “Please a bama yarinyar nan barka da salla. Na manta ban bata ba”.        Malam ƙarami da ya fahimci Nu'aymah yake nufi sai yay murmushi. bai musa ba ya amsa yay masa godiya, dan suma daya basu sukaƙi amsa a ciki ɓata rai yayi, wai basu ɗaukesa ɗan uwansu ba. Hakanne ya sakasu amsa tunda yace barka da salla ce.          Duk abinda ke faruwa Solomon na saurarensu. Dama cike yake da haushin sake zuwa wannan gidan. Ya kuma ɗauki alwashin suna komawa wannan karon sai ya sanarma madam Chioma. Dan tsaf ya fahimci waɗan nan mutanen zasu iya jan hankalin Ogan nasu tsaf, musamman yanda suke masa hidima kamar wani sarki. Yanzu haka a gabansa aka saka babbar leda a booth wai kayan barka da salla ne aka bama Yoohan ɗin a cikin gida. Ya cije bakinsa yana satar kallon Yoohan daya kwantar da kansa jikin kujera ya lumshe idanu kamar mai barci ta mirror.           Babu abinda kema Yoohan kai kawo a zuciya da ruhi sai kalaman Nu'aymah. Kalaman sunyi masifar tasiri a ransa fiye da zaton mai karatu. Sai faman tisasu yake dalla-dalla kamar mai bitar karatu. Duk da ac dake aiki a motar bai hana zufa tsatstsafo masa a goshi ba. Mafarkin da yayi shekaran jiya da baba malam ya kuma sake maimaita shi yau da safe ya shiga tariyowa shima.               ya sauke wani irin nannauyan numfashi yana sake tariyo mafarkin nasa da yayi a karo na biyu kenan,         *Ya kanga kansa a mafarkin a gaban wani kogo ƙaton gaske, cikinsa akwai wani irin wuta dake ci mai ban tsoro, dan duk iya hasashensa ya kasa kamanta ƙarfin wutar da zafinta a zahiri. Aduk lokacin da yake a gaban wannan kogon dake zuwa masa a mafarki, ya kan tsinci kansa cikin matsanancin mawuyacin hali da ruɗu, sai dai kuma abin mamaki sai ya ga baba malam acan gefensa cikin shiga ta kamala, a wasu irin korayen ciyayi masu bada ni'imtaccen yanayi yana masa murmushi da miƙa masa littafin nan na musulmai (Al-Qur'ani), yakan ringa ce masa_______*         *_“Yoohan wannan shine zancen ALLAH, littafi dake ƙunshe da kowane irin sirri, littafin da aka aiko MANZONMU ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) da shi. kanada sauran daman riƙo dashi domin ka samu tsira daga wannan narkon azabar dake gabanka. Kazo gareni, zan nuna maka hanyar sanin UBANGIJINA kamar yanda ya aiko MANZONMU ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) a garemu ya nuna mana muma, ya kuma koyar damu. Ni Sooraj bin Hashim, na rantse maka da ALLAH, babu wani addini na gaskiya sai musulinci, babu wata hanya ƙyaƙyƙyawa sai ta bin UBANGIJI, babu wani abin taƙama da riƙo sai MANZON ALLAH. Inhar kabi ALLAH, kai koyi da koyarwar MANZON ALLAH, ka riƙe gaskiya da amana, ka tsare gangar jikinka daga saɓama ALLAH, ka nema dukiyarka ta hanyar halak, kaji tsoron zalintar mutane, ka kiyaye jinka da ganinka daga haramun, ALLAH bazai jarabceka da shiga wannan taskar azabar dake a gabanka ba. Domin UBANGIJI ya tanadi gidaje guda biyu, WUTA DA ALJANNAH, ya kumayi alƙawarin cikasu da mutane. Dan haka Yayha kazo gareni, kazo ka karɓi kalmar LA'ILAHA ILLAH, MUHAMMADURRASULULLAH (S.A.W)._*           A wancan ranar da yay wannan mafarki ya wayi garine a yanayin sanyin jiki, da tunane tunane kala-kala. Ya kuma yini zuciyarsa na rinjayarsa da amsa wannan kira. Sai dai daya tuna wani gagarumin al'amari sai yay azamar ƙwaɓar kansa harma da alƙawarin nisanta kansa da su baba malam ɗin. Dan yau ɗin nanma da ƙyar manager ya lallaɓa shi sukazo nan ɗin. duk da kuwa yana a cikin kanon yau kwanansa biyu kenan ma.        Kafin su ƙarasa hotel ɗin daya sauka sosai ya tsinta kansa cikin ruɗanin kalaman Nu'aymah da mafarkinsa. Sai ɗunbin takaici da dana sanin abinda ya aikata ma yarinyar yakeyi, wanda sam ba halinsa bane yin hakan, amma yasan ita da duk wanda zai iya ji ko ganinsu a lokacin bazai taɓa yarda da shi ba. Ya ɗan ciza leɓensa na ƙasa da ƙarfin tsiya, ƙirjinsa na sake masa zafi.      Motocin na tsayawa baiko jira an buɗe masa ba ya buɗe da kansa ya fice. Daga Solomon har sauran guards ɗinsa tsaye kawai sukai suna kallonsa cike da mamaki da tsoron yanayin nasa. Da sauri Solomon yabi bayansa shima dan yasan ba lafiya ba dai. Gashi key ɗin ɗakin Yoohan ɗin yanama a hannunsa ne.      Ɗan gudun da yayine ya sakashi cimmasa. Dan haka suka ƙarasa ƙofar ɗakin tare. Solomon ya buɗe masa tare da matsawa ya bashi hanya dan ya shiga.         Batare da yace masa komaiba ya shige, shi ma Solomon ɗin sai ya bisa yana faɗin, “Sir lafiya kuwa?”.         Cak Yoohan ya tsaya da ga yunƙurin shiga Bedroom ɗin da ya keyi, batare da ya juyoba ya ɗagama Solomon ɗin hannu da masa alamar ya barsa.       Da baya-baya Solomon ya rinƙa tafiya harya fice da ga ɗakin, yaja masa ƙofar a hankali gabansa na faɗuwa da yanayin ogan nasu.............✍ 🤔🤔🚶🏻Tofa, Dr Yoohan yaya dai?🚶🏻 _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻. [5/18, 12:14 PM] Amina Mama: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*. No. 29 .............“Na faɗaɗa maka muhimmanci kalmar shahada ne domin kasan addinin musilinci ba abin wasa bane, sannan bautama UBANGIJI shi kaɗai bashi da abokin tarayya shine cikakken imani. Gujema shirka babba da shirka ƙarama domin dawwama da tsira wajen bautama ALLAH shi kaɗai da tabbatar da soyayyar MANZONMU a zukatanmu wajibine. Zaka karɓi kalmar shaha yanzun nan Yahya, da ga haka ka tabbatar kabar kafircema ALLAH har abada, ka tsarkake ranka da zuciyarka cewa babu wani sarki sai ALLAH, ANNABI MUHAMMADU kuma MANZON ALLAH ne”.      Kai Yoohan ya jinjina a hankali, zuciyarsa na wani irin tsitstsinkewa, tsigar jikinsa na tashi batare da yasan dalili ba. Hakama jininsa gudu yake a cikin jijiyoyinsa da sauri-sauri. Wannan yanayin sai ya saukarma jikinsa da kasala da wani rauni da bai taɓa tsintar kansa a ciki ba.      Baba malam na faɗar kalmar shahada yana maimaitawa, suna kai ƙarshe sai kawai hawaye suka ɓalle masa tamkar an buɗe fanfo. Ya sakko a kujerar da yake zaune a hankali ya durƙushe ƙasa jikinsa na wani irin rawa. A matuƙar mamakin su baba malam sai gani kawai sukai ya kai goshinsa ƙasa yayi sujda.        Ɗan yatsa baba malam ya saka ya ɗauke hawayen da suka sakko masa gefen ido kaɗan. Hakama Abban Abdallah sai da hawaye suka cika masa idanu, sai jin wata irin ƙauna da soyayyar Yoohan ɗin suke tana nunkuwa a zukatansu. Kamar yanda shima ƙaunarsu ke sake masa ninƙaya a zuciya.        Koda ya ɗago da ga sujudar da yayi kamar yanda yaga baba malam yayi ɗazun sai kawai ya matsa ya rungume baba malam ɗin yana cigaba da hawaye. Sunja tsahon lokaci a haka kafin baba malam ya ɗagosa yana murmushi, yace,           “Yahya ina tayaka murna. akwai ayyuka sosai a gabanka. Amma kafin su yanzu zakayi wankan shiga musulinci”.       Cikin lunshe idanu dajin wata nutsuwa ta musamman Yoohan ya gyaɗa masa kai.        Bisa jagorancin baba malam Yoohan ya gabatar da wankan shiga musilinci, tare da tsaftace wasu najasosi dake jikinsa, kamar tarin gashin kansa, an ragesa, amma ba sosai ba, dan baba malam ya shaida masa barin gashi ado ne, sannan koyine da MANZON ALLAH (S.A.W), bama ason ayi aski tas-tas ɗin nan kai na ƙyalli. Yanke masa ƙunba. Duk da shi bama mutum bane mai tarata, tare da sauran abubuwan da suka dace su kasance a tsaftace ga ƙa'idar musilinci.      Bayan ya shirya tsaf cikin sabuwar suturarsa farar ɗanyar shadda tas, da taji ɗinkin da yay masa ɗas a jiki baba malam suka rungumesa suna sake masa marhaban da shigowa addinin gaskiya, sannan suka sake zama da shi a karo na biyu domin masa bayani akan SALLAH.       yanzu kam harda su Abba Musbahu suma sun shigo tawagar. Bayan an kawo musu breakfast sunci tare su biyar abin sha'awa. Bayyana muku irin farin cikin da nutsuwa da Yoohan ke ciki a wannan lokaci ɓata lokaci ne.      Shiru falon ya ɗauka duk suna sauraren baba malam dake zuba bayani cike da nutsuwa da ƙwarewar ilimi da sanin da ALLAH ya azurtashi da shi.        Yoohan! Sallah na nufin addu'a. Amma a shari'ance ibada ce ma'abociyar karatu da ayyuka Keɓaɓɓu, da ake fara ta da kabbara a kuma rufe ta da sallama, sallah ita ce rukuni na biyu a cikin Addinin Musulunci bayan kalmar shahada, wato *_(ASH'HADU AN LA ILAHA ILALLAHU WA ASH'HADU ANNA MUHAMMADAN RASULULLAH)_* sai ita. kuma ita ce kashin bayan addini, saboda girmanta da matsayinta ALLAH bai aiko mala’ika da ita ba sai ALLAH Madaukakin Sarki Ya kirawo ANNABI (SAW) a daren Isra’i da Mi’iraji ya bashi ita. Yana daga girman sallah ambatonta da ALLAH Madaukakin Sarki Yayi sau hamsin da takwas (58) a cikin Alkur’ani, kamar inda yake cewa: {وَأَقِيمُوا الصَّلَوةَ} [البقرة: 43] Ma'ana: "Ku tsaida sallah" {قُلْ لِعِبَادِيَ الَّذِينَ آمَنُوا يُقِيمُوا الصَّلَوةَ}[إبراهيم: 31] Ma'ana: "Ka fada (Ya Muhammad S.A.W) ga bayina da suka yi imani su tsaida sallah". Da sauran wurare a cikin Alqur'ani da dama. Annabi (SAW) yana cewa: “Bainar rajuli wabainal kufri tarkus salati” (Rawahu Muslim).       Ma’ana: “Tsakanin mutum da kafirci shine barin sallah”. Kuma ana umartar karamin yaro da yin Sallah tun yana dan shekara bakwai, kuma in ya kai shekara goma a doke shi in ya ki yi.      Sallah bata yiwuwa sai da alwala.   ALWALA: Ubangiji Madaukakin Sarki yana cewa: "يأيها الذين ءامنوا إذا قمتم إلى الصلوة فاغسلوا وجوهكم وأيديكم إلى المرافق وامسحوا برءوسكم وأرجلكم إلى الكعبين وإن كنتم جنبا فاطهروا وإن كنتم مرضى أو على سفر أو جاء أحد منكم من الغائط أو لامستم النساء فلم تجدوا ماء فتيمموا صعيدا طيبا فامسحوا بوجوهكم وأيديكم منه ما يريد الله ليجعل عليكم من خرج ولكن يريد ليطهركم وليتم نعمته عليكم لعلكم تشكرون" المائدة: 6. "Ya ayyuhal lazina aamanuu izaa kumtum ilas salati fagsilu wujuuhakum wa’aydiyakum ilal maraafiki wamsahuu biru’uusakum wa’arjulakum ilal ka’abayni wa’in kuntum junuban faddahharuu wa’in kuntum marda au alaa safarin au ja’a ahadun minkum minal ga’idi au laa mastumun nisa’a falam tajidu ma'ana fatayammamu sa’idan dayyiban famsahuu biwujuuhikum wa’aydiykum minhu maa yuridul Laahu liyaj’ala alaykum min harajin walakin yuridu liyudahhirakum waliyutimma ni’imatahu alaykum la’allakum tashkuruun”. Alma’ida: 6.          “Yanzu zamuje kaga yanda ake alwala kafin salla”. Baba malam ya faɗa yana miƙewa. Gaba ɗaya suka biyosa ƙofar toilet ɗin dake cikin falon. Yayinda Yoohan da baba malam suka kasance daga ciki.        *YADDA AKE YIN ALWALA SHINE:*       1-Da farko yin niyya a zuci sannan ka ce: “Bismillahi” sannan ka wanke tafukanka na dama da na hagu kowanne sau uku(3).      2-Sannan ka debo ruwa ka kurkure bakinka ka zubar da ruwan sau uku(3).      3-Sannan ka debo ruwa ka shaka a hanci ka fatar shi ma sau uku(3).       4-Sannan ka debo ruwa ka wanke fuskarka gaba dayanta sau uku(3), a lura cewa wanke fuska yana farawa ne tun daga farkon goshinka har izuwa karkashin haba wato kusa da makoshi a tsayinta kenan, a fadi kuma tun daga gefen kunnen dama zuwa gefen kunnen hagu.      5-Sannan a wanke hannu tun daga tafuka har zuwa gwiwar hannu na dama da na hagu shima uku(3).       6-Sannan a ɗebo ruwa a yi shafar kai wato a tafin hannu a shafo tun daga farkon goshi har a kai ƙeya sannan a sake dawowa farkon goshi.        7-Sannan shafar fatar kunnuwa na dama da na hagu.      8-Sannan a wanke kafafu na dama da na hagu tun daga tafin kafa har izuwa gwiwar kafa.           *ADDU’A BAYAN KARE ALWALA:* "أشهد أن لا إله إلا الله وحده لا شريك له وأشهد أن محمدا عبده ورسوله" رواه مسلم. "سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك" رواه الطبراني. “Ashhadu an Laa ilaha illal Lahu wahdahu laa sharika lahu wa’ashhadu anna Muhammadan abduhu warasuluhu”. Muslim ne ya rawaito.         Ko kuma ka ce; “Subhanakal Lahumma wabihamdika Ashhadu an Laa ilaha illa anta astagfiruka wa’atubu ilaika”. Dabarani ne ya rawaito.        “Wannan itace alwala Yahya. Da ita ake gabatar da bautar ALLAH, idan babu ita babu salla. Akwai abubuwan da suke warwareta, amma zamu ajiyesu zuwa nan gaba a neman ilimi zaka sansu. A yanzu muna tsinkayar jiran shigar lokacin azhar ne, dan a ƙa'ida ko wanne wuni musulmai na gabatar da salla sau biyar ne. Akwai nafiloli da mutum kan ƙara dasu domin samun kusanci ga UBANGIJI. Amma da waɗan nan biyar dazan lissafa maka sune wajubabbu. Wanda ya barsu ko yayi sakaci dasu, haƙiƙa bai cika cikakken musulmi ba.        *SALLOLI  WAJIBABBU:* Ya zo a hadisin Dalhatu bin Ubaydullah cewa: "أن أعرابيا قال: يا رسول الله ماذا فرض الله عليَّ من الصلاة؟ قال: «خمس صلوات في اليوم والليلة.. الحديث… Ma'ana: "Cewa wani Balarabe ya ce: Ya Ma'aikin ALLAH me UBANGIJI (SWT) ya wajabta a garemu na daga sallah? Sai ANNABI (SAW) ya ce: Salloli biyar a cikin (kowane) wuni da dare".        Salloli wajibabbu guda biyar sune: 1-Asubah, 2-Azzahar,  3-La'asar,  4-Magriba,  5-Isha'i.           *LOKATAN  SALLAH  DA ADADINSU:* ASUBAH: Sallah ce da ake yin ta raka'a biyu, Lokacin yin ta kuma shine bayan bullowar alfijir na gaskiya. Sannan ana yin karatunta a bayyane, Fatiha da sura a kowacce raka'a sannan a yi tahiya ayi sallama. AZZAHAR: Sallah ce da ake yin ta raka'a hudu, Lokacin yin ta yana farawa idan rana ta bar tsakiyar sama ta karkata zuwa mafadarta. Sannan ana yin karatunta a asirce, Fatiha da sura a raka'o'in biyun farko, sai a zauna a yi tahiya, sannan Fatiha kadai a raka'o'in biyun karshe, sannan a sake yin tahiya a yi sallama. Amma a ranar Juma'a sallar Azzahar tana zamowa sallar Juma'a a inda take komawa raka'a biyu kuma ana yin karatunta a bayyane, bayan liman ya kare khuduba. LA'ASAR: Sallah ce da ake yin ta raka'a hudu, Lokacinta na farawa daga inda inuwar abu tayi daidai da tsayinsa. Sannan ana yin karatunta a asirce, Fatiha da sura a raka'o'in biyun farko, sai a zauna a yi tahiya, sannan Fatiha kadai a raka'o'in biyun karshe, sannan a sake yin tahiya a yi sallama. MAGRIBA: Sallah ce da ake yin ta raka'a uku, lokacin yin ta shine idan rana ta fadi a mafadarta (a nan Najeriya fuskar yamma). Sannan ana yin karatun raka'o'i biyun farko a Fatiha da sura amma a bayyane, sai a zauna a yi tahiya sannan a mike a yi raka'a daya ta karshe a karanta Fatiha kawai a asirce, sannan a sake yin tahiya a yi sallama. ISHA'I: Sallah ce da ake yin ta raka'a hudu, Lokacinta yana farawa ne idan shafaki ya buya (wato dan jaja-jajan nan na bayan faduwar rana idan gari ya fara duhu). Sannan ana yin karatunta raka'o'in biyun farko Fatiha da sura a bayyane, sai a zauna a yi tahiya, sannan Fatiha kadai a raka'o'in biyun karshe a asirce, sannan a sake yin tahiya a yi sallama. *KIRAN SALLAH:* الله أكبر الله أكبر أشهد أن لاإله إلا الله أشهد أن لاإله إلا الله أشهد أن محمد رسول الله أشهد أن محمد رسول الله حى على الصلاة حى على الصلاة حى على الفلاح حى على الفلاح الله أكبر  الله أكبر لا إله إلا الله Allahu Akbar, Allahu Akbar, Ash-hadu an La’ilaha Illal-lah, Ash-hadu an La’ilaha Illal-lah, Ash-hadu anna Muhammadar-Rasulullah, Ash-hadu anna Muhammadar-Rasulullah, Hayya alas-Salat, Hayya alas-Salat, Hayya alal-falah, Hayya alal-falah, Allahu Akbar Allahu Akbar La’ilah aillall-lah. Wannan shi ne lafazin kiran sallah. An so ga wanda ya ji kiran ana kiran sallah ya maimaita abin da mai kiran sallar yake fada shi ma, sai a wajen fadin "HAYYA ALAL SALAT" da kuma fadin "HAYYA ALAL FALAH" a madadin ka maimaita su idan mai kiran sallah ya fade su, sai ka ce "LA HAULA WALA KUWWATA ILLA BILLAH". *YADDA AKE YIN SALLAH:* - Da farko sai ka fiskanci alkibla (Saitin inda Ka’aba take, anan arewacin Najeriya ana cewa Gabas domin nan ne saitin inda Ka’aba take daga nan) sai a yi ikama, ga yadda lafazinta yake:         Allahu Akbar, Allahu Akbar, Ash-hadu an La’ilaha Illal-lah, Ash-hadu anna Muhammadar-Rasulullah. Hayya alas-Salati. Hayya alal-falahi. Kad-kamatis-salatu, Allahu Akbar, Allahu Akbar, La’ilah aillall-lahu.        Sai ka daga hannuwanka daidai kafadunka ko daidai kunnuwanka sai ka yi Kabbara wato ka ce: “Allahu Akbar”.        -Sai ka dora hannunka na dama akan hannunka na hagu a kirjinka (kabalu), ko kuma ka sake su (sadalu), duk wanda ka yi daidai ne.       -Sai ka karanta karatun bude sallah a asirce ake yinta ita ce: “Subhankal Lahumma wabihamdika watabaraka ismuka wata’ala jadduka wala’ilaha gairuka”         ko kuma ka ce: “Allahumma ba’id baini wabaina hadayaya kama ba’adta bainal mashriki wal magribi, Allahumma nakkini min hadayaya kama yunakkal saubul abyadi minad danasi, Allahumma agsilni bil ma’i wassalji wal baradi”.         -Sannan a karanta Fatiha zuwa karshenta.       -Sannan a karanta abinda ya sauwaka na daga Alkur’ani sura ko wani sashi na sura daga Alkur’ni.        -Sai ayi kabbara “Allahu Akbar” ayi ruku’u, a cikin ruku’u ana iya karanta: “Subhana Rabbiyal Azim Wabihamdihi” ko a karanta “Subbuhun Kuddusun Rabbul Mala’ikati Warruhu” gwargwadon abinda ya sauwaka.       -Sai a dago daga ruku’u ana fadar "Sami'al Lahu Liman Hamidahu" idan an dago an tsaya kafin a tafi sujjada sai a ce: “Allahumma Rabbana walakal hamdu” ko ka ce “Rabbana walakal hamdu”         -Sai kuma ayi kabbara “Allahu Akbar” a yi sujjada ana fadin “Subhana Rabbiyal A’ala wabihamdihi” a cikin sujjada gwargwadon abin da ya sauwaka a (a lura cewa sujjada ana yinta akan gabobi guda bakwai, goshi tare da hanci, tafuka biyu, guiwoyi biyu da kuma kafafu biyu).        -Sai ayi kabbara “Allahu Akbar” a dago daga sujjada a zauna akan kafar hagu ko duwawun hagu, a dora tafuka akan cinyoyi ana fadin “Rabbigfirli” ko kuma “Allahumma Igfirli”.      -Sannan ayi kabbara “Allahu Akbar” a koma sujjada ta biyu ana fadin “Subhana Rabbiyal A’ala wabihamdihi” a cikin sujjadar gwargwadon abin da ya sauwaka. -Sannan a yi kabbara “Allahu Akbar” a dago daga sujjada ta biyu, yayin mikewa zuwa raka’a ta biyu (idan an zauna dan kadan kafin mikewa raka’a ta biyu ba laifi, ana kiran wannan dan zama kadan “jalsatul istirahati”).    Sai a sake kawo raka’a kamar yadda aka yi wannan ta farko, amma idan an dago daga sujjada ta biyu a raka’a ta biyu sai a zauna kamar irin zaman da aka yi na dagowa daga sujjada ta farko a dora hannaye akan cinyoyi, sannan hannun dama ayi nuni da dan yatsa manuniya a yi karatun tahiya a wannan zama, karatun tahiya shine:        “Attahiyatu Lillah, Azzakiyatu Lillah, Addayyibatus Salawatu Lillah, Assalamu alaika ayyuhan Nabiyu Warahmatullahi Wabarakatuhu, Assalamu Alaina wa’ala ibadil Lahis Salihina, Ash’hadu an La’ilaha illal Lahu Wa’ash’hadu anna Muhammadan Abduhu warasuluhu”.       Haka ya zo a (Muwadda Malik, lafazin Umar bn Khaddab).   Idan sallar mai raka’a biyu ce, kamar sallar Asubah sai ka cikasa karatun tahiyar anan da salati Ibrahimi. Shi ne kamar haka:       “Allahumma salli ala Muhammadu wa’ala aali Muhammad kama sallayta ala Ibrahim wa’ala aali Ibrahim innaka Hamidun Majid, Wabarik ala Muhammad wa’ala aali Muhammad kama barakta ala Ibrahim waala aali Ibrahim Innaka Hamidun Majid”.        Sai kayi sallama, ka ce “Assalamu Alaikum Warahmatullah”. Ko kuma ka yi sallamar bangaren damanka da kuma hagunka.        Idan kuma sallar mai raka’a uku ce kamar Magariba ko raka’a hudu kamar Azahar da La’asar da Isha’i, idan kayi kashi na farko na karatun tahiya sai ka tashi ka cikasa ragowar raka’ar da ta rage ko daya ko biyun (a lura cewa a ragowar raka’ar da ta rage bayan biyun farko Fatiha kadai za’a karanta ban da sura ko wani sashi na sura) sai ka sake zama na tahiya a karo na biyu ka cikasa tahiyar har zuwa sashi na biyu na salati Ibrahimi sannan ka yi sallama ka ce “Assalamu Alaikum Warahmatullah” Ko kuma ka yi sallamar bangaren damanka da kuma hagunka.         *BAYANIN SHARADAN SALLAH Sharadan sallah sune:-* 1.Musulunci. (ba ta inganta ga wanda ba Musulmi ba).        2.Hankali (ba ta inganta ga mara hankali).      3.Tsarkin dauda: Shine tsarkake jiki da tufa da bugire na mai sallah tun daga farawa har kammalawa.     4.Tsarkin Hadasi: Shine duk abin da ke warware alwala, shima tun daga fara sallah har zuwa kammalawa. Ana bukatar wadannan tsarki a cikin kowace irin sallah ma’abociyar raku’i da kuma sujjada kai har ma wanin nan nata.         5.Shigar lokacin sallah. 6.Niyya.      7.Sitirce al’aurar namiji tana kamawa ne daga cibiya har zuwa gwiwa. Ita kuwa mace baki dayan jikinta al’aurane ga ajnabinta sai dai fuskarta da tafukan hannuwanta.      8.Fuskartar Alkibla; Sai dai in a halin rincabewar yaki ko nafila a tafiyar da ya halatta ayi kasaru kuma mutum ya zamo mahayi ne kan abin hawa.      Wanda ya yi sallah yana kallon watan alkibla ba yana mai mantawa ko rashin sani har sai da ya yi sallama, to ya saketa har abada, sai dai malamai sun yi sabani a cikin wannan hukunci, haka hukuncin ya ke idan ya zamo bai yi sani da alkiblar ba ko ya ganganta yin sallar ba a alkiblar ba.        “Yahya musulinci yana da ƙa'idoji da tsare-tsare ga komai na rayuwa musamman ma ibada. Wannan kaɗanne daga ciki nake tsakuro maka a yanzu, kafin kayi ninƙaya cikin taskar ilimi ka fahimci manufata. Inaga yanzu mataki na gaba da zamuje domin gabatowar Azhar shine karantar fatiha daga littafin ALLAH, wato Al-qur'ani. Sauran abinda zai biyo baya zamu bisa daki-daki mu tsara yanda zaka samu karantarsu. Dan zamu sake komawa baya muyi cikakken bayani akan tsarki a muhimmancin sa. Ina fatan kana fahimtar duk abinda mukeyi”.          Cikin raunin murya da sanyin gaɓoɓi Yoohan ya amsa da, “Ina fahimtar komai Uncle, ina kuma cikin ɗunbin farin ciki da kasancewata cikin wannan addini dake cike da tarin hikimomi da ƙa'idoji ababen birgewa da ƙayatarwa. Tabbas tun a yinin farko na fara cin karo da ni'imomin musulinci, ina fata da addu'ar cigaba da karo dasu har ƙarhen numfashina. A yau ina jina tamkar wani sabon hallita, tamkar ba Yoohan Goshpower ba, lallai babu abinda ya kai addinin musulinci nutsuwa da kwanciyar hankali. Ya ALLAH na gode maka da wannan ni'ima taka, ina roƙon ka cigaba da tabbatar da ita a gareni batare data yanke ba koda a sakan guda ne na rayuwata”.       Cike da farin ciki su Baba malam suka amsa masa. Handkherchief Yoohan yasa ya ɗauke hawayen da suka ciko masa idanu. Kafin ya durƙusa har ƙasa yana godiya gasu baba malam da suka zamewa rayuwarsu sandar jagora wajen jawosa daga DUHU zuwa HASKE.       Saurin ɗagosa baba malam yay ya runmesa. “Yahya bamu bane ALLAH ne, mu kawai mun kasance ne daga cikin ƙaddararka ta alkairi, ALLAH yayi maka albarka, ya share hawayenka, ya yaye maka damuwarka, ya karɓi tubanka, ya shafe zunubanka damu baki ɗaya”.       A tare suka sake amsawa da amin. __________★★★★__________                 A hotel kam hankalin su Solomon a matuƙar tashe yake da rashin ganin Yoohan. Gaba ɗaya sun tada hankalin ma'aikatan hotel ɗin da barazanarsu. Saboda maigadi ya tabbatar shi baiga fitar Yoohan ba. Hakama wanda yake a reception yace baiga fitarsa ba. Ga kuma motocinsu duk suna ajiye alamar Yoohan bai fitaba a fahimtarsu.         Ganin ƙaramar magana na neman zama babba Solomon ya kira papa ya sanar masa halin da ake ciki. Cikin matsanancin tashin hankali papa yace su kira layin Yoohan ɗin mana.          “Sir! Duk wayoyinsa na nan cikin ɗakin, shiyyasama muka fahimci bada kansa ya fitaba kenan”. Solomon da jikinsa har tsuma yake ya bama papa amsa murya na rawa. Wata wawiyar tsawa papa ya sake daka masa daga can, tare da sakin wani irin ihu tamkar zai fasa gidan.        “Solo!!!!!! Inhar yarona ya shiga wani hali na rantse muku da ALLAH duk sai na kasheku da hannuna, na baku awa biyar kacal akan nemansa. Idan har kuka bari na iso kano kuyi kuka da kanku!!....”     Ƙit ya yanke wayar batare da ya bari Solo yay ko ƙwaƙwaran numfashi ba.         Sosai hankalin Solomon ya sake ƙololuwar tashi, hakama na sauran ƴan uwansa. Dan sunsan wanene Pastor Goshpower, sun san kuma abinda zai iyayi, musamman ma akan Yoohan da duk duniya bai haɗa sonshi dana kowa ba.        Suna cikin tashin hankali da tararrabin mafita sai ga ƴan sanda kusan mota uku sun iso hotel ɗin bisa jagorancin D.p.o Emanuel.      Su masu hotel babban tashin hankalinsu kar sunansu ya ɓaci. suko su Solomon sune sukasan babban tashin hankalin da zai iya samunsu da su kansu masu hotel ɗin indai har ta tabbata anyi kidnapping ɗin Yoohan a hotel ɗin ne, kamar yanda kowa yake tunani da hasashe.............✍ [5/18, 12:14 PM] Amina Mama: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta_*. No. 27 ............Zubewa Yoohan yayi a saman gadon tare da saurin dafe kansa dake barazanar rabewa biyu, sai kuma ya ɗan naushi gadon da faɗin, “Noooo!!!”. Da ƙarfi kamar mai magana da wani.     Tashi yay zaune zumbur yana huci, so yake abinda ya faru yabar ransa, amma tamkar ana ƙara kusanto masa da hotonsa ne a zuciya. Da ya rufe ido babu abinda yake gani sai yana kissing ɗin yarinyar da ko sunanta baima sani ba. Miƙewa yay daga gadon ya shiga toilet ɗin dake cikin ɗakin, ko takalman dake ƙafarsa bai cireba balle kuma kaya, ya ƙarasa gaban shower ya tsaya, tare da kai hannu ya murza makunnar da ƙarfi, tamkar itace tai masa laifi.      Shaaa!!! Ruwa ya fara sauka masa bisa gyararren gashinsa yana gangarowa fuska. Lokacin da ya gangara cikin jikinsa ya wani saki sassanyar ajiyar zuwa tare da lumshe idanunsa ya dafe bangon da hannunsa duk biyu. A haka ruwan ya cigaba da sauka a kansa, kafin wani dogon lokaci ya gama jiƙewa sharkaf. Sai da yay kusan mintuna ashirin a haka sannan ya kashe shower ɗin yana sauke numfashi a jajjere, kafin ya ƙarasa saman toilet sit ya zauna yana mai riƙe kansa da hannu biyu.... _______________________           Duk yanda Nu'aymah taso sakewa a sashen Addah ta kasa hakan. Gani take kamar kowa yasan abinda ya faru tsakaninta da Yoohan. Kamar an tsikareta ta miƙe daga zaunen da take kusa da Kubrah. Dukansu da kallo suka bita har suna rige-rigen tambayarta lafiya.     Sai da taɗan saci kallon Addah da tai banza dasu kafin ta amsa musu cike da in-ina. “Um.....u.... Zanje su Aunty Zulfah na jirana”. Bata jira amsar su ba tai wuf ta nufi ficewa da ga falon tamkar zata kifa dan sauri.      Karo suka kusan ci da Malam ƙarami da ke shigowa. Tai saurin komawa da baya tana faɗin, “Yi haƙuri Yaya, bansan ka taho ba”.      Murmushi ya mata da cewa, “Karki damu Aymah. Ashe dama kina nan naje nemanki wajen Umm”. Ɗan kallonsa tayi kamar zatai magana sai kuma ta fasa. Ya sake faɗaɗa murmushin sa, “Dama ba wani abu bane, baƙon da kika ganmu tare a sashen Hajjo ne ya bada barka da salla a baki. Shine naje kai miki na Iske baƙya nan. Amma na bama Umm ta ajiye miki”.       Tunda ya ambaci baƙo gabanta ya sake tsananta faɗuwa. Ta tsaresa da manyan idanunta dake wani mar-mar na rashin gaskiya. Sai kuma ta ɗan juya ta kalli sashen da su Addah suke. Su dukansu hankalinsu na wajen. Sai taji hankalinta ya sake tashi. Tai saurin faɗin, “Ni banaso Yaya”.     Kafin yayi magana ta fice da gudu daga falon. Shi malam ƙarami ma dariya abin nata ya bashi. Hakama su Hajarah. Dan haka suka shiga ƙyalƙyala dariya banda Kubrah da tai shiru tana kallon wani waje daban.      Hajarah ce ta fara farga da yanayin Kubrah, dan haka ta tsagaita da tata dariyar tana faɗin, Aunty Kubrah ALLAH dama nasan ba ciwon kai Nu'aymah keyiba. Inagafa sabon siriki ta samo ma su Addah shine duk take a ruɗan nan”.     Uffan Kubrah batacema Hajarah ba. Sai ma mikewa tai ta bar falon tana wani ɗan murmushin da su duka basu fahimci ma'anarsa ba...... Nidai nace, “Humm”.         “K lafiya? Kika shigoma mutane tamkar wadda aka koro!”. Umm ta faɗa a tsawace tana kallon Nu'aymah data shigo falon a guje.       Duƙar da kai tayi ƙasa tana ƙoƙarin haɗiye kukan da ke son zubo mata. Cikin rawar murya tace  “Umm babu komai fa, zanje toilet ne”. Bata jira amsar kowa ba a cikinsu ta shige ɗakinta da sauri.       Dariya su Aunty Zulfah sukayi, sai dai banda Umm da tabi Nu'aymahn da ido dan sam bata yarda da abinda ta faɗa ba.             Tana shiga toilet ɗin ta maida ƙofar ta rufe harda murza key. Jingina tayi da ƙofar ta fashe da kuka maiban tausayi. A ranta tana faɗin yaya zatai da wannan abin kunya da takaici da mutumin nan ya aikata a gareta? Ita namiji yayma kiss, namijinma kafiri da baya bautama ALLAH. Baisan idan ya saɓama UBANGIJI ba ya nema gafara. Baisan haramci ba baisan halacci ba, balle yasan hukuncinsu. Bakinda bai taɓa ambaton ALLAH ba sai shan giya da zina, bakin dake ambaton wanin ALLAH (Shirka) shine yau akan nata. ‘ALLAH ya isa bazan taɓa yafe makaba’. Ta faɗa a fili tana sake rushewa da kuka. ‘Na shiga uku ni Zainab, ni.........’        “Nu'aymah!”. Muryar Umm ta hanata ƙarasawa. Saurin toshe bakinta tayi dan kar Umm taji shashshekar kukanta.       “Nu'aymah wai baƙya jinane?”. Umm ta sake faɗa tana matsowa jikin bayin.       Da sauri Nu'aymah tai gyaran murya. Kafin ta miƙe da sauri gaban tap ta fara wanke fuskarta, kallo ɗaya taima mirror tasan idan Umm ta ganta a haka akwai matsala, to amma kuma bata da wani ikon ko dabarar yin wanka tunda yanzu nan tayi sa. Towel tasa ta tsane fuskar tata sannan ta buɗe ƙofar a hankali ta fito.       Haɗa ido sukai da Umm da ke a tsaye tana jiran fitowar tata. Tai saurin kauda idanunta zuwa ƙasa da faɗin, “Umm yi haƙuri, ALLAH toilet ne”.          “Toilet ko kuka?”. Da sauri ta ɗago ta kalli Umm ɗin. Muryarta na rawa tace, “Umm toilet ne ALLAH”.       “Toilet ɗin ki kai ma kuka kenan?”. Baki taɗan tura gaba, “To Umm gudawa fa ce”.         “Mtsoww! K dai bansan randa zaki bar wannan shashancin ba wlhy. Idan gudawan ne bazaki iya zuwa ki amshi magani ba”.          “Kiyi haƙuri Umm”. Juyawa Umm tayi ta fice batare data tanka mataba. Itama sai ta sauke ajiyar zuciya tanabin mahaifiyar tata da kallo. Ta tabbatar yau da tasan mita aikata da saita fasa mata baki. Dan Umm tana da zafi idan aka ƙureta, sam bata ƙaunar halin banza.          Duk da tana buƙatar kaɗaici haka ta daure ta sake gyara fuskarta sannan ta fito falon. Dan bata fatan wani ya gano halin da take ciki. Musamman ma Umm data kasance mace mai saurin fahimta akan rashin gaskiyar yaranta. Ba komai ya jawo hakanba kuwa sai saka musu ido da takeyi a duk motsinsu kwarai da gaske. (Iyaye ya kamata mu kasance haka. muzama kowanne motsin yaranmu nakan idanunmu da zukatanmu kodan gudin yin tufƙa da warwara akan tarbiyyarsu. ALLAH ya kare mana su dai damu baki ɗaya).      Tana zama aunty Rafi'a tace, “Hummm! Aymah ina kika samo wannan turaren mai shegen daɗi haka?”.      Gaban Nu'aymah yay mugun faɗuwa. Ta ɗago da dauri tana kallon aunty Rafi'a. Sai taga har Umm ma ashe kallonta take tamkar yanda su Aunty Zulfah duk suka xuba mata idanu. Ta buɗe baki zatai magana su Nanah suka shigo cikin uhun sallama.        Wata muguwar ajiyar zuciya Nu'aymah ta sauke a ɓoye. Tare da saurin miƙewa zumbur ta nufi su Nanah ta rungume.            Zuwan su Nanah gidan ne ya shashantar da maganar turare. Amma ga Umm sam abin yaƙi barin ranta. Dan sai da tai duk dabarar da uwa ta gari ya dace tayi wajen shaƙar ƙamshin a jikin Nu'aymah. Ta kuma jisa, ta tabbatar duk gidan kuma batasan kowa da wannan ƙamshin ba. Amma sai bataima Nu'aymah maganar ba. Dan tuni su Nanah sun janyeta ma sun fice su da su Amal daga gidan.        ____________________        Ya jima zaune matuƙa akan toilet sit kafin ya miƙe ya fara zame jiƙaƙƙun kayan jikinsa. Wanka yayo, ya fito sanye da Bathrobe fara mai ɗan tsaho. Dan ta wuce gwiwarsa kaɗan. Towel ƙarami ya riƙo a hannu ya fito yana goge fuskarsa da sumarsa.         Kallo ɗaya yayma Solomon daya kasa haƙuri ya dawo ɗakin duk da korar da yay masa ya ɗauke kansa. Kan Solo a ƙasa yace, “Kamin afuwa Sir, bazan iya nutsuwa ba bayan kai kana cikin wani hali”.        Yanzun ma uffan baice masa ba. Ya dai gitta ta gabansa ya wuce zuwa gaban kujeru biyu dake a ɗakin. Zama yay cikin ɗaya ya ɗora ƙafafunsa saman table ɗin dake a gabansu tare da naɗe towel ɗin hannunsa saman kansa ya jingina bayansa da kujerar ya lumshe idanu.      Shi dai Solomon na tsaye yana cigaba da kallonsa cike da damuwa. A can ƙasan ransa kuwa zargine fal ciki akan su baba malam. Gani yake kamar yau rashin bin Yoohan cikin gidan yasa aka cutar da shi........        “Ina buƙatar coffee”. Ya katsema Solomon tunaninsa cikin yin magana a daƙile.     Da sauri Solo ya dawo hankalinsa. Ya amsa da “Okay sir” yana matsawa inda telephone ɗin ɗakin take yay kira domin yin order ɗin coffee ɗin da Yoohan ya buƙata.       Ba'afi mintuna uku zuwa huɗu ba kuwa sai ga cikin ma'aikatan yay knocking. Solomon ne ya je ya buɗe ya amso. Ya dawo inda Yoohan ɗin ke zaune ido a lumshe ya ajiye tray ɗin ƙasa dan ya ɗaura ƙafarsa akan table ɗin. Saida ya tsiyaya masa, tare da saka sukari ƙwara ɗaya kamar yanda yasan Yoohan na buƙata sannan ya miƙa masa.       “Gashi Sir” ya faɗa da yarensu. Buɗe ido Yoohan yay a hankali. Sunyi jajur alamar baya cikin nutsuwarsa. Baice komaiba ya amsa tare da yima Solomon alamar yaje. Badan Solo yaso hakanba ya fito yana waigensa. A falo ya maƙale dan bazai iya zuwa ko inaba yabar Yoohan ɗin a haka, kodan gudun ɓacin rai mai tsanani da zai iya fuskanta a gurin madam Chioma da Papa.          Yoohan da baisan Solomon bai fitaba ya fara shan coffee ɗin a hankali zuciyarsa na cigaba da kai kawo akan abubuwa masu yawan gaske. A haka ya shanye ya sake zubama kansa. Yanzu kam ko sugan ma bai sakaba a haka ya sha kayansa. Koda ya gama kuma nan ya cigaba da zama har tsahon lokaci.        Zuwa can kuma tamkar wanda aka mintsina sai ya miƙe, duk da rigar wanka ce a jikinsa bai damu ba, a haka ya buɗe ƙofar ya fice bayan ya zura Slippers. Tsaye yayi yana kallon Solo dake gyangyaɗi a falo, kansa ya ɗan girgiza ya nufi ƙofa batare da yayi magana ba.          Can ya fita harabar hotel ɗin da ko ina ke ƙwanyar da haske, mutane nata kai kawo tamkar ba dare ba. Mafi yawansu mazane dake shigowa da mata. Wasu kuma matan su kaɗai ke shigowa alamar masu jiran nasu suna ciki su. Wasu mazan kuma su kaɗai ne suma, dan wasu matafiyane ba sheɗancin ne ya shigo dasu ba.          Watsar da komai yay dan shi baya matsama kansa shiga hurumin da banasa ba. Can wajen kujerun da aka tanada dan hutawa ya nufa. Babu mutane sosai a wajen, dan haka ya samu ɗaya ya zauna, tare da sake tsunduma cikin abinda ke masa kai kawo a zuciya da ruhi tun ɗazun.        A cikin tunanin nasa ne hankalinsa ya fara karkata ga abinda na kusa da shi ke saurare a wayarsa. Duk da ya saka ƙarar can ƙasa sosai hakan bai hana Yoohan ji ba saboda dare ya fara nisa. Wajen da suke kuma wajene da sam babu hayaniya, dan hotel ɗin dama bana ku bayi bane, na manya ne masu ji da ƴan canji, inda aka ginasa ma kawai ya isa baka amsa.           Lecture ce da ga bakin Sheikh Fantami yake saurara. Kasancewar da turanci ne sai komai yake shiga kunnen Yoohan raɗam. Buɗe idanu yay a hankali ya kai dubansa ga mai sauraren wa'azin. Matashin saurayine tamkarsa, sai dai kallo ɗaya zakai masa kasan kaga ustaz. yayi shiru a wajen tamkar baisan da motsin kowaba yanata sauraren wa'azin sa.       Tsintar kansa yay shima da sake nutsuwa sosai yana saurare. ya shagala sosai da sauraren wa'azin nan mutumin ya miƙe, batare da yayi tunanin wani na tayasa ji ba ya kashe tare da barin wajen ya koma ciki dan ya kwanta ya huta.        Ko kaɗan Yoohan baiso hakan ba, dan anzo wata gaɓa da duk mai sauraren wa'azin zai so jin ƙarshensa. Bin mutumin yayi da kallo harya ɓacema ganinsa. Ji yay tamkar ya bisa ya roƙe ya basa ya ƙarasa ji. Dan jikinsa wani irin tsuma ya keyi, gashi duk ya mimmiƙe masa. Komai ya sake birkice masa, duk yanda yake tunanin tasirin mafarkinsa da maganganun Nu'aymah sai lecture ɗin nan daya saurara ta sake faɗaɗa rauninsa zuwa ƙololuwar rikicewar tunani da gushewar wani duhu daya fahimci ya jima a cikinsa. Tunanin bin bayan mutumin ya sakashi kallon agogon hannunsa, ya ɗan waro idanu waje dan bai ankaraba sai yaga agogo ya nuna ƙarfe ɗaya saura.          Sake maida idanunsa yay ya lumshe tamkar baiga mi agogon ya nuna masa ba. Sai ajiyar zuciya daya dinga saukewa a jajjere.          A haka Solomon daya sake shiga ɗakin nemansa bai gansaba ya fito a rikice nemansa ya iske sa. Duk da wayar dake a hannunsa da alama ta nuna wanine akan layin sai da ya sauke ajiyar zuciya .          “Ashe kana anan sir?!”. Solo yay maganar yana sake sauke numfashin ruɗanin da yake ciki na rashin ganin nasa da farko.          Yoohan da tun isowar Solomon wajen yana kallonsa ta ƙasan ido ya buɗe idanunsa ya watsa masa wani shegen kallo mai cike da gargaɗi.....         “I'm sorry sir. Madam ce”.         Kafesa da ido sosai yayi, duk da kuwa yasan Momy Solomon ɗin ke nufi. Bai amshi wayarba, bai kumace komaiba ya miƙe yabar wajen. Solo dake binsa da kallo yay saurin bin bayansa hankali a tashe.          Koda suka koma ɗakin bai gajiya ba sai da ya sake maimaita masa maganar amsar wayar sannan ya miƙa masa hannu alamar ya bashi. Yana amsar wayar ya nunama Solo toilet da hannu.      Duk da bai fahimcesa ba haka ya nufi toilet ɗin dan ya duba. Shi kuma ya ɗora wayar saman kunnensa muryarsa mai amo da kauri ɗin nan ta fara fidda sauti. “Hello Mom”.     Ajiyar zuciya mai ƙarfi madam Chioma ta sauke da ga can, kafin cikin ƙasa da murya sosai tace, “My boy!”.        “Humyim”. Ya faɗa a hankali cikin maƙoshi.       Murmushi mai sauti ta sake da ga can tana mai ƙanƙame filo a ƙirjinta da lumshe idanu. Cikin sake narke murya tace, “Mike damunka?”.       Shiru yay na wasu sakanni. kafin ya furzar da ɗan huci yana sauke idanunsa da ga table ɗin. “Ba komai Mom, bakiyi barci ba?”.            Sake narke murya tayi kamar zatai kuka. Tace, “My Boy tunaninka ya hanani barci. Kai kasan muna tsananin buƙatar ganinka tare da mu ni da papan ku dama ƙannenka gaba ɗaya. Amma duk da ɗokin dawowarka da mukeyi wannan karon, bayan tsahon sati biyu da ka ɗauka bakanan shine kai wucewarka wani gari batare da ka fara sauka Abuja mun ganka ba”.          “Am so sorry Mom”. Ya faɗa a taƙaice kawai.      Matse filo ta sakeyi sosai a ƙirjinta. Dan ji take jininta na wani masifar yamutsawa tamkar zaiyi tsartuwa ya fito. Kafin ta samu damar sake magana ta sake tsinkayar muryar Yoohan na faɗin, “Mom goodnight, zan kwanta”. Ƙitt ya yanke wayar.       “My b......” tai yunƙurin faɗa sai kuma taji ƙitt. Da sauri ta ciro wayar daga kunnenta ta kalla. A take fuskarta tai masifar tsukewa hawaye na taruwa mata cikin idanu. Filo ta sake jawowa zata ƙanƙame papa ya shigo ɗakin nata.        “Wai lafiya kika maƙale anan bayan inata jiranki a can?”.      Wani irin takaici da baƙin ciki ne ya kumeta a zuciya. Ta ɗan hararesa a kaikaice tana maijin wani irin zafinsa da ɗaci a ranta. Amma a zahiri sai tai ɗan murmushi da cewa, “Ka bari kawai. Solomon ne ya kirani wai yaga kamar John a damuwa. Shine fa nasa ya haɗamu dan wayoyinsa duk basa tafiya. Amma yaron nan sai ya amsa ni sama-sama. daga ƙarshe ma ya yanke wayar”.       Ƴar dariya Papa dake hawowa gadon yayi. ya jata jikinsa ya rungume yana faɗin, “Kema kinsan halin yaronki ai. Minene zai ɓata miki rai a ciki. Maybe yana buƙatar hutawa ne shiyyasa ya kashe”.     Kafin ta samu damar basa amsa ya haɗe bakinsu waje guda. Duk yanda taso ta ƙwace kanta ya hanata wannan damar. Dan dama inhar ALLAH ya bashi sa'a a kanta baya wasa da damarsa. Saboda duk lokacin da zai buƙaci kasancewa da ita sai sunsha uwar rigima, wani lokacinma ƙarfi yake nuna mata ya samu nutsuwa. Yakan rasa miyasa take masa hakan tunda shi dai yasan auren soyayysa sukayi. ada can kuma sam bata masa wannan halin sai a shekarun nan da bazasu gaza goma zuwa sha ɗaya ba.     To komadai minene yau ya moreta da ƙyau. Daga ƙarshe ya koma lallashinta sabida kuka da take masa tamkar wanda yay mata fyaɗe. Da ƙyar ya samu kuwa tai shiru sukai barci duk da shi ya rigatayi kafin itama ya sacetan.          Yoohan kam koda ya yanke wayar sai yay jifa da ita saman kujerar dake gefensa. ya sake maida kansa jikin kujerar ya lumshe idanunsa tamkar ɗazun.      A haka Solomon da ya kammala tattare kayan da Yoohan ɗin ya baza a toilet ya fito ya samesa. Baiyi magana ba, ya lallaɓa kawai ya ɗauki wayarsa ya fice da ga ɗakin. Duk da Yoohan najinsa bai motsaba, haka ya cigaba da zama a wajen har tsahon lokacin da shima kansa baisan ya kai ba, dan barci ne mai nauyi ya kwashesa a wajen, tare da faɗawa cikin nannauyan mafarki maiban tsoro da al'ajabi a garesa.            Gabannin asuba ya farka a firgice, da ƙyar ya iya motsa wuyansa da ya ƙage, cikin dauriya da jarumta ya shiga jujjuyasa yana matse fuska saboda zafi. Sai da yaji ya ɗan sake masa sannan ya miƙe tsaye yana sauke tagwayen ajiyar zuya. Duk da a zuciyarsa yayi mamakin barcin da yay a zaune na kusan awa huɗu sai baiyi magana ba ya taka a hankali zuwa gaban Window. Idanu ya rufe zai fara addu'a kamar yanda sukeyi a addininsu sai kuma yay saurin buɗewa. Hannu ya saka ya buɗe Window ɗin. Sassanyar iskar asubahi ta feso masa, tare da ƙwala kiran sallar farko da ga wani massallaci da alamu suka nuna yana gab da hotel ɗine ko kuma a cikin hotel ɗinma yake . Wani wawan numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa. Haka kawai sai ya tsinci kansa a wani irin nishaɗa na musamman..............✍ _____________________________ ZAFAFA BIYAR 2021 _______________________                     Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻. [5/18, 12:14 PM] Amina Mama: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*. No. 28 ............Sake buɗe idanun yay ya saukesu bisa giza-gizai dake yawo cikin hasken sararin samaniya na yanayin asubahi. Karan farko a rayuwarsa da zuciyarsa ta tafi wajen tunanin da girmama UBANGIJI da ya halicci sammai, gata dai babu icce ko ɗaya daga kowacce kusurwa ta duniya da zakai zaton ta riƙeta. Sannan babu wata sarƙa ko ƙarfe da suma suke amsa sunan ginshiƙi a gareta. Da rana hasken *_Rana_* ya mamayeta. Da dare hasken *_Wata_* ya ƙawata ta da adon taurari. da *_Damuna_* na _Giza-gizai_. Lokacin asubahi takan canja kala zuwa sky blue da wasu ado masu ban mamaki da al'ajabi. Hakama da yammaci lokacin faɗuwar rana takan ƙawatu da kalar sky blue da na yanayin faɗuwar rana. Duk wannan hikima da rahamar akan azurtamu da sune babu ko naira ɗaya. Babu kuɗin haraji babu na ƙarshen wata. To miyasa wanda ya azurtamu da ita bai taɓa jiran mu biyasa da ko taro ba?  ‘saboda shi ɗin *_(SARKI NE GAGARA MISALI DA BAUTA KAWAI AKE KAƊAICE SA)’_*          Wani yanki na zuciyarsa ya bashi wannan amsar.        Samun kansa yay da sake lumshe idanu ya sauke wasu tagwayen ajiyar zuciya saboda wata kalma data faɗo cikin kunnensa daga massallacin da aka kira salla dan sun saka tafsir ne.. (Kana son sanin ni'imar dake cikin addinin musulinci?). Furicin ya fito daga bakin Sheikh Sooraj Hashim jibiya (Baba malam) dan sun saka tafsir ɗin nasa ne.          ‘Tabbas ina son sanin ni'imar dake cikin addinin musulinci?’. Ya amsa tamkar shi ɗin akeyima tambayar kai tsaye. yana mai cigaba da kallon yanda wata keyin ƙasa cikin giza-gizai alamar lokacin faɗuwarsa yayi, zai bama rana guri itama tazo ta cika umarnin ALLAH (S.W.A) akan aikinta.         Tabbas wannan tambaya ta tsayama Yoohan a zuciya. Dan da ita ya ƙarasa sauran daren daya rage masa. Akan kunnensa har aka kira assalatu akai salloli a massalatai. Sai da gari yay haske sosai sannan ya iya barin jikin Window ɗin zuwa toilet.      Ji yake a ransa bazai taɓa samun nutsuwa ba sai ya dangane da gidan baba malam a safiyar nan. Dan tabbas yana buƙatar sanin (Hanyar fahimtar ni'imomin dake cikin addinin musulinci? A yau).        A gaggauce ya gudanar da komai. Kamar ko yaushe yay shirinsa cikin ƙananun kaya. Blue jeans da farar shirt mai gajeren hannu. Sai ya ɗora suit jacket fara tas itama. Yau dai bai saka necktie ba, maɓallin shirt ɗinma ba duka aka rufe ba. Cikin ƙamshinsa ya baro cikin hotel ɗin batare daya nema inda su Solomon suke ba.          Safiya ce sosai a garin, hakan yasa da ƙyar ya samu keke napep, shima da mutum ɗaya a ciki. Bai damu ba, duk da kuwa wannan shine karan farko a tarihin rayuwarsa da zai shiga napep ɗin. Lokacin da mai napep ya tambayesa ina zasa? Da ƙyar ya iya haɗa hausan ya bashi amsa da sunan baba malam kawai. Dan dama bawai ya iya hausan bane yana dai jin abubuwa sosai saboda mu'amula da mutane marasa lafiya akan aikinsa. Sai dai bai iya maidawa, bayan gaisuwa sai abubuwan da baza'a rasaba suma ɗai-ɗai ne.      Sai da aka fara ajiye wanda ya tarar a ciki kafin shi a kaisa. Kusan dubu uku ya miƙama mai napep ɗin. Da mamaki shiko yake kallonsa, yama rasa mizai ce masa dan ya fahimci hausa ba isarsa tayi ba. Sake miƙo masan da yayne ya saka mai napep ƙoƙarin haɗa ɗan turancinsa ya sanar masa naira ɗari da hamsin ne kuɗinsa. Duk da dai turancin bai haɗu da ƙyau ba Yoohan ɗin ya fahimci mi ya faɗa. Dan haka ya ajiye masa kuɗin a jiki yana faɗin, “Na baka ne duka”. Yanda yay maganar da hausa abin dariya, harma mai napep ya kasa haƙuri sai da ya dara.        Yoohan baibi takansa ba ya nufi ƙofar gate ɗin su baba malam kansa tsaye, kai kace gidansa yazo.                Sau uku yay Knocking sannan maigadi ya buɗe ƙaramar ƙofar ya leƙo yana tambayar “Wai wanene haka da farar safiyar nan?” dan yasan su Baba malam ta ƙaramin gate sukaje massallaci yau.      Bai gane Yoohan ba. Dan duk zuwan da yay har sau biyu bashi kaɗai ya shiga ba sai da jagorancin masu gidan. Sai da ya gama ƙare masa kallo sama da ƙasa kafin yace, “Samari lafiya kuwa? Mikake nema ko buƙata anan?”.         Sam Yoohan bai fahimta ba, bayan kalmar (lafiya da wasu ɗai-ɗai) babu abinda ya gane a zancen maigadi. Sai yay shiru yana kallonsa cike da nazarin miya kamata ya ce da shi. Maigadi da haushi ya kama ya sake maimaita masa tambayar?. Nan ɗinma dai ba fahimtar yayi ba. Sai ma ya jefa masa tambaya da turanci shima.       “To bakajin hausa kenan?”. Maigadi ya faɗa a hankali. Sai kuma ya kalli Yoohan yay masa alama da hannu (wai yana zuwa). Kafin Yoohan ɗin yace wani abu maigadi ya koma ciki. Saurin yunƙurowa Yoohan ɗin yayi zai tsaidashi sai dai tuni ya rufe ƙofar.       Cike da damuwa ya dafe kansa. Sai kuma ya juya yana kallon titin anguwar. babu mutane sosai, sai tsilli-tsilli dake fitowa cikin massallacin. Sai kuma sautin karatun yara da shima alama ta nuna daga harabar massallacin ne.        Nufar gate ɗin massallacin yayi, kasancewar shi a buɗe yake sai ya samu damar shiga kansa tsaye. Sai dai bai kai tsakkiyaba wani cikin almajiran malam ya tsaidashi da sauri, dan kallo ɗaya zai tabbatar maka Yoohan ɗin ba musulmi bane.       Anyi sa'a almajirin malam najin turanci, sannan kuma duk zuwan da Yoohan yayi gidan sau biyu ya gansa. Ba ƙaramin daɗine ya kama Yoohan ba jin cewar almajirin malam najin yaren da shima yake ji. Cikin sauƙi suka gaisa ya sanarmasa wajen malam yazo. Kuma yana cike da ƙaguwar san ganinsa domin dalilin babban uziri.          Duk da almajirin malam yayi mamaki hakan bai hanashi yarda zaima Yoohan ɗin iso ba. Dan haka ya nuna masa wani ɗan dakali alamar ya zauna ya jurasa. Shi kuma ya juya cikin massallacin inda yasan malam na zaune yana karatu da azkar kafin ya fara karatu ga magidantan anguwar dakan ɗauki karatun safe da baya wuce zaman awa guda.          Yoohan bai zauna ba. Sai ma faman bin massallacin yake da kallo. A ransa yana sake jinjina ƙoƙarin da su baba malam sukai wajen ginashi. Dan ƙaton gaske ne, kuma ya ginu da gini mai ƙyau. Gashi an shafesa da farin fenti yanata ɗaukar ido tamkar ba'a shiga cikinsa, sai shukoki da suka sake ƙawata shi suma. Ko ina kuma a tsaftace yake. Daga wajen da yake tsaye yana shaƙo daddaɗan ƙamshin dake fitowa daga massallacin wanda kullum safiya da maraice Nu'aymah ke zuwa ta sharesa ta saka turaren wuta da kalolin Air Fresheners masu daɗin ƙamshi..........      Kukan wani yaro ne ya katse masa tunanin nasa. Ya ɗan juya inda yake jiyo kukan. Hakan yayi dai-dai da fitowarta daga cikin ajin da take koyarwa riƙe da bulalar dorina. Sanye take da dogon hijjabi mai hannu fari tas dan har yana jan ƙasa. Hannunta na dama riƙe da Al-qur'ani, na haggu kuma bulala. Yanda take jijjiga bulalan tana magana da nuna yaron ne ya sakashi shagala da kallonta. A ransa ya raya, ‘Ashe kowa ma masifa take masa?’. Jiba dai yanda takema yaro ƙarami duk da kuwa bayajin mi take faɗa. Amma yanayinta ya nuna faɗa takeyi dan tama saka yaron kneeling ne a ƙofar ajin.........        “Yahya! kai ne da safen nan?”. Maganar baba malam ta katsesa daga kallon Nu'aymah daya shagala yi. Numfashi ya sauke tare da juyowa ga baba malam ɗin. Baba malam daya juya yana kallon abinda Yoohan ɗin ya shagala kallo shima ya ɗauke kansa ya maido garesa. Sake mai-maita masa tambayar yayi a karo na biyu.          Yoohan da ya sunkuyar da kai ƙasa yace, “Uncle, inason sanin minene ni'imomin dake a cikin addininku na musulinci?!”.         Ba baba malam da yayma tambayarba, hatta Abban su Abdallah dake fitowa daga massallacin sai da ya taka wani uban birki.       Baba malam da jikinsa ya hau tsuma yace, “Yoohan sake maimaitawa naji”.      Babu musu Yoohan ya kuma faɗin,                “Ina son sanin ni'imar dake cikin addinin musulinci?!”.     الْحَمْدُ للهِ الَّذِي بِنِعْمَتِهِ تَتِمُّ الصَّالِحَاتِ . Alhamdu lillahil-lazee bini’imatihi tatimmus-salihat.         Godiya ta tabbata ga ALLAH wanda saboda ni'imarsa ce kyawawan ayyuka suke cika. اَلْحَمْدُ ِللهِ عَلَى كُلِّ حَالٍ. Alhamdu lillahi ala kulli halin         Godiya ta tabbata ga ALLAH a cikin kowane hali.         Sai ya durƙusa a ƙasa yay sujida hawaye na sauka masa a fuska.       Yoohan dake binsa da kallo yay saurin duƙawa shima yana zaro manyan idanunsa a waje. durƙushewa yay gwiwa bibbiyu yana kallon malam harya ɗago daga sujidar da yay.      Fuskarsa ɗauke da murmushi ya kama Yoohan suka miƙe tare, sai kawai ya jawosa jikinsa ya rungume.      Duk da ba yaune karan farko da aka fara yima Yoohan irin wannan rungumar ba sai yaji ta yau ɗin kamar daban ce a rayuwarsa. Kamar ba irin wadda Papa da sauran mutane ke masa bace. Kamar girman ta yau ɗin na musamman ne.      Baba malam ya ɗagosa da sauri tare da riƙe hannunsa. Yace, “Lallai yau zaka fara sani da ga rahamar UBANGIJINA, domin kuwa, *HASKE da RAHAMAR UBANGIJIN* al'arshi ta bayyana a zuciyarka da harshenka Yahya!. Sai dai bazaka taɓa fahimtar tarin ni'imomin dake cikin musilinci ba daga wajensa har sai ka shigo cikinsa”.        Yoohan da bai fahimcesa ba yay shiru yana kallonsa ƙasa-ƙasa. Sai kusan seconds goma ya ɗago kaɗan ya kalli baba malam ɗin da ƙyau, sai kuma ya sake maida kansa ƙasa. “Uncle ban gane mikake nufi ba”.      Murmushi baba malam yayi, ya sake gyara tsaiwarsa cikin harshen turancin da suke magana yace, “Ina nufin bazaka taɓa fahimtar ni'imomin dake tattare da wannan addini mai daraja ba har sai ka kasance musulmi Yoohan. Ta wannan hanyar ne kawai zaka ƙwanƙwaɗi madarar ni'imar UBANGIJI fiye da zaton hasashen ka”.         Babu ko tantama Yoohan yace, “Inhar zan sani ɗin ta wannan hanyar zan biya ko nawane na shiga addinin naku dan na sani, dan na tabbatar idan ban sani ɗinba natsuwa zata cigaba da yin nisa da ni har abada”.        “UBANGIJI kai ne gagara misali a tunanin hankali ko hasashen zuciya. Tabbas kai mai ikone ga wanda kaso, a kuma lokacin da kaso. Yahya shiga addinin musilinci ba'a biyan ko sisi. *_ALLAH maɗaukakin sarki ya halicci halitta ne domin su bauta masa, kuma ya sawwake musu abinda zai taimaka musu na arzikinsa, ALLAH maɗaukakin sarki yana cewa:_*       _“Kuma ban halicci aljan da mutum ba sai domin kawai su bauta mini. Bana neman wani arziki daga gare su kuma bana bukatar da su ciyar da ni. Lalle ALLAH shi ne kaɗai mai azurtawa kuma ma’abocin karfi sosai”._ Suratuz Zariyat, aya ta:56-58.         *_Mutum a halittar da ALLAH ya yi masa zai bautawa ALLAH ne shi kaɗai inda za’a bar shi, ya zama mai son ALLAH ya na bauta masa ba ya yi ma sa shirka, sadai abinda ya ɓata wannan (dabi’ar) kuma yake karkatar da ita shi ne abin sheɗanun aljanu da na mutane su ke ƙawata mata na abinda sashin su yake yi wa sashi wahayi na ƙawatacciyar Magana kawai don ruɗi, shirka wata aba ce da ta zo daga baya kuma ta kutsa kai ga halittar da ALLAH ya yi wa mutum, ALLAH maɗaukakin sarki yana cewa:_*       _“To, ka tsayar da fuskarka ga wannan addini kana mai kaucewa shirka, halittar ALLAH wacce ya halicci mutane a kan ta, babu mai canza halittar ALLAH”._ Suratur Rum, aya ta: 30.    *Kuma Ma’aikin ALLAH (S.W.A) ya ce: “Dukkan abin haihuwa ana haihuwarsa ne akan musulunci, to iyayan shi ne su ke yahudantar da shi, ko su Nasarantar da shi (kiristan da shi) ko su majusantar da shi”. Bukhari da Muslim ne su ka ruwaito.*        Dan haka Yahya UBANGIJI baya buƙatar ko sisi da ga gareka face amsa kalmar *_La'ilaha illallah......._*”.        Sosai abin ya bama Yoohan mamaki da wannan bayani na baba malam. dan haka ya gyaɗa kansa yana mai gyara tsaywarsa da faɗin, “Na shirya amsar wannan kalma Uncle”.        Murmushi sosai ya sake faɗaɗa a fuskar baba malam, batare da ya sake cewa komai ba ya kama hannun Yoohan sukabi ta ƙaramar ƙofa zuwa cikin gida. Abban su Abdallah na biye da su zuciyarsa fal tunanin inda ya taɓa sanin mai kama da Yoohan ɗin a wasu shekarun baya..         Sashen mahaifinsu kai tsaye suka nufa, ko ina fes yake dan ana gyarawa saboda sukan zauna a ciki musamman randa sukaso nishaɗi. Duk hidimar bikin salla ma jiya a ciki sukayita su huɗun. Sai da duk suka zauna, Yoohan da Abban Abdallah kowa nama ɗan uwansa kallon sani baba malam ya katsesu da faɗin.      *_“Shaidawa Babu Abin Bautawa Da Gaskiya Sai ALLAH, Kuma Muhammadu MANZON ALLAH ne”_*.        _“Waannan kalmomin shahada guda biyu, sune ƙofar shiga musulunci, sune kuma rukuninsa mafi girma, kuma ba a yin hukunci da musulusncin mutum, sai da furuci da su, da kuma aiki da abin da suka ƙunsa, da wannan ne kuma kafiri yake zama musulmi._        1-Ma’anar kalmar shahada: Ma’anar shaidawa da cewa babu abin bauta da gaskiya sai ALLAH, shi ne yin furuci da ita tare da sanin ma’anarta, da kuma yin aiki da abin da ta ƙunsa, zahiri da baɗini, malamai sun haɗu akan cewa furuci da kalmar shahada, ba tare da sanin ma’anarta ko yin aiki da abin da ta ƙunsa ba, ba shi da amfani, kai sai dai ma ta zama hujja a kansa, kuma ma’anar (La Ilaha Illallah) shi ne babu abin bautawa da gaskiya sai ALLAH shi kaɗai matsarkaki maɗaukaki.        _Rukunan wannan kalmar (shahada) sune: (korewa da tabbatarwa), wato kore haƙƙin bauta daga wanin ALLAH, kuma tabbatar da shi ga ALLAH shi kaɗai ba shi da abokin tarayya. Haka kuma wannan kalmar ta ƙunshi kafircewa ɗagutu (shi ne dukkannin abin da ake bauta masa wanda ba ALLAH Maɗaukaki ba, ko da kuwa ya kasance mutum ne (tare da yardarsa da bautar da ake masa), ko dutse, ko bishiya, ko son zuciya, ko sha’awa), da nuna masa ƙiyayya da yin kuɓuta daga gare shi._         *_Wanda ya faɗi wannan kalmar (shahada da bakinsa) amma bai kafircewa abubuwan da ake bauta musu wanin ALLAH ba (a aikace), to tamkar bai faɗeta ba. ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Kuma abin bautarku abin bauta ne guda ɗaya. Babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Mai rahama Mai jin ƙai”.(Baƙara: 163)._*        *_Kuma Maɗaukaki ya ce: “Babu tilastawa game da (shiga) addinin (musulunci), haƙiƙa shiriya ta bayyana daga ɓata, saboda haka wanda ya kafirce wa ɗagutu kuma ya yi imani da ALLAH, to haƙiƙa ya riƙi igiya amintacciya, (wadda) ba ta yankewa. ALLAH kuwa Mai ji ne, Masanine”._* (Baƙara: 256)            _Kuma kalmar (Ilah) tana nufin abin bautawa da gaskiya, duk wanda ya ƙudurci cewa abin da ake nufi da kalmar (Ilah) shi ne: Mai halitta, Mai arzutawa, ko wanda yake da ikon ƙirƙira, kuma ya ƙudurci cewa yin imani da wannan kawai zai wadatar, ba tare da kaɗaita ALLAH da ibada ba, to haƙika faɗin kalmar (La Ilaha Illallahu) ba za ta amfane shi ba, a nan duniya wajen shiga Musulunci, kuma a Lahira ba zata kubutar da shi ba daga azaba madawwamiya._          ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Ka ce (da su): “Wane ne yake arzuta ku daga sama da ƙasa? ko kuma wane ne yake mallakar ji da gani?, kuma wane ne yake fitar da mai rai daga matacce, ya kuma fitar da matacce daga mai rai? Wanene kuma yake tsara al’amura?” To za su ce: “ALLAH ne”. To ka ce (da su): yanzu ba za ku ji tsoronsa ba?” (Yunus: 31).          *_ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Ko wane ne ya halicci sammai da ƙassai, ya kuma saukar muku da ruwa daga sama, sannan (da wannan ruwan) muka tsirar da (shukokin) gonaki masu ƙayatarwa, ba kuwa za ku iya tsirar da bishiyoyinsu ba?, shin akwai wani abin bautawa tare da ALLAH, A’a, su dai mutane ne da suke kauce wa (gaskiya)”. (Naml: 60)._*          Kuma ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Kuma lallai idan ka tambayesu, “Wanene ya halicce su?, Lallai za su ce: “ALLAH ne” To, yaya ake juyar da su (daga bauta wa ALLAH)?” (Zukhruf: 87).            *_“Ma’anar Shaidawa Lallai MUHAMMADU MANZON ALLAH ne:_*         _Ma’anar shaidawa lallai (Annabi) Muhammadu MANZON ALLAH ne shi ne a yi masa biyayya cikin abin da ya umarta, da gaskatashi a kan abin da ya ba da labari, da nisantar abin da ya hana kuma ya yi tsawa a kansa, kuma ba za a bautawa ALLAH ba sai da abin da ya shar’anta._        *_Tabbatar Da Shaidawa Lallai MUHAMMADU MANZON ALLAH ne:_*       _ MANZON ALLAH ne: Shaidawa lallai (Annabi) Muhammdu Manzon ALLAH ne tana tabbata ne da yin imani da cikakken yaƙinin cewa lallai (Annabi) Muhammdu tsira da amincin ALLAH su tabbata a gare shi bawan ALLAH ne, kuma Manzonsa ne ya aiko shi zuwa ga Aljanu da mutane gaba ɗayansu, kuma lallai shi ne cikamakin Annabawa da Manzonni, kuma shi Annabi tsira da amincin ALLAH su tabbata a gare shi bawa ne makusanci a gurin ALLAH ba shi da komai daga siffofin ALLAH, kuma (wannan shaidar tana tabbata ne) da yi masa biyayya da girmama umarninsa da haninsa, da lazimtar sunnarsa a baki, a aikace, kuma a ƙudurce._        *_ALLAH ya ce: “Ka ce: ya ku mutane lallai ni MANZON ALLAH ne zuwa gare ku gaba ɗaya” (A’araf: 158). _*      _Kuma ya ce: “Ba mu kuma aiko ka ba face zuwa ga mutane baki ɗaya, kana mai gargaɗi da bushara” (Saba’a: 28)._        _Kuma ya ce: “(Annabi) Muhammadu bai kasance uban ɗaya daga mazajenku ba, sai dai (shi) Manzon ALLAH ne kuma cikamakin Annabawa” (Ahzab: 40)._          _Kuma ya ce: “Ka ce tsarki ya tabbata ga Ua UBANGIJINA, ni ba kowa ba ne face mutum kuma Manzo” (Isra’i : 93)._       Wannan (tabbatar da shaidawa Annabi Muhammadu Manzon ALLAH) ya ƙunshi al’amura kamar haka:        Na farko: yarda da Manzoncinsa da ƙudurceshi a ɓoye cikin zuci.       Na biyu: yin furuci da haka da harshe a bayyane.       Na uku: koyi da shi da yin aiki da abin da ya zo da shi na gaskiya, da barin abin da ya hana na ƙarya.         *_ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Sai ku yi imani da ALLAH da Manzonsa, Annabi Ummiyyi¹, wanda yake imani da ALLAH da kalmominsa, kuma ku bi shi don ku shiriya” (A’araf: 158)._*       Na huɗu: gaskatashi a kan dukkan abin da ya ba da labarinsa.    Na biyar: Mutum ya so shi sama da son kansa da dukiyarsa da ɗansa da mahaifinsa da mutane baki ɗaya; domin shi MANZON ALLAH ne, kuma haƙiƙa sonsa yana daga cikin son ALLAH, da so saboda ALLAH Haƙiƙanin son MANZON ALLAH shi ne yi masa biyayya wajen bin umarninsa da nisantar haninsa da taimakonsa da jibintarsa.          *_ALLAH ya ce: “Ka ce: idan kun kasance kuna son ALLAH, to ku bi ni, sai ALLAH ya so ku, ya kuma gafarta muku” (Ali Imran: 31)._*            Kuma ANNABI tsira da amincin ALLAH su tabbata a gare shi ya ce: “Ɗayanku ba ya zama mumini har sai ya soni fiye da mahaifinsa da ɗansa da mutane gaba ɗaya” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi daga hadisin Anas ALLAH ya yarda da shi.        *Kuma Allah Maɗaukaki ya ce: “Saboda haka waɗanda suka yi imani da shi, suka kuma girmama shi, suka kuma taimake shi, suka kuma bi hasken da aka saukar a tare da shi, to waɗannan su ne marabauta” (A’araf: 157).*        Na shida: Ƙudurce cewa sunnarsa asali ce ga shari’ar musulunci, kuma ita sunnar kamar Alƙur’ni mai girma take (wajen dogoro da aiki da ita), saboda haka ba a saɓa mata domin hankali ya ci karo da ita.        Na bakwai: yin aiki da sunnarsa da gabatar da maganarsa a kan maganar kowa, da miƙa wuya zuwa gare shi, da yin hukunci da shari’arsa da yarda da ita.         *_ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Na rantse da girman UBANGIJINKA ba za su yi imani ba, har sai sun sanyaka mai hukunci game da abin da ya faru a tsakaninsu, sannan kuma ba su sami wata ƙunci ba a zukatansu game da abin da ka hukunta, su kuma miƙa wuya gaba ɗaya” (Nisa’: 65)._*...............✍ ZAFAFA BIYAR 2021 Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[5/19, 6:47 PM] Amina Mama: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*. No. 31 ..............Ta ƙaramin gate Yoohan yay ficewarsa. Hakan yasa Kubrah data biyo bayansa ta rasa ina ya nufa. Har babban gate taje bayan ta gama dube-dube a harabar gidan bataga wata baƙuwar mota ba duk saina ƴan gidan.              Yanda ta iso gate ɗin a rikice tana tambayar maigadi sai abin ya bashi mamaki. Amma sai kawai ya bata amsa da cewar babu wanda ya fita.        “What?! Yama zakace dani babu wanda ya fita a gidan nan? Bayan nasan tabbas idan ba fitaba babu inda zai nufa”.        “Hajiya Kubrah wlhy babu wanda ya fita kamar yanda na sanar miki. Shin kodai ɓarawo ne ya shigo gidan ban sani ba?”.       Wani takaicine ya sake tuƙe Kubrah, batare data bashi amsaba ta bar wajen tana zuba masa harara. Shima tsit yayi bai sake magana ba, sai dai zuciyarsa fal saƙe-saƙe. ★★★★             Yoohan na fitowa waje yay turus dan mamakin ganin motocin gidansu da alamu suka nuna tsayawarsu kenan. Dan yanzu suke ƙoƙarin fitowa. Mamaki yay masifar sake kamashi ganin papa harda d.p.o Emanuel da yaransa. Tsuke fuska ya sakeyi ya nufesu ganin yanda suka tafi kai tsaye ga gate ɗin gidan dan su basu ganshi ba.        “Papa!” ya faɗa dai-dai lokacin da papa ya kai hannu zaiyi knocking gate ɗin. A kusan tare duk suka juyi garesa domin shigar muryarsa mai amo da kauri cikin kunnuwansu.         Wata wawuyar ajiyar zuciya suka shiga saki a jajjere, musamman ma guards ɗin Yoohan da suka san suna a cikin gagarumin tashin hankali inhar ba'a samesa anan ɗinba.        Papa har yi yay tamkar zai kifa dan saurin zuwa ga Yoohan ɗin. Yay wani bala'in rarumosa jikinsa ya rungume yana faɗin, “Thanks you lord. my son are you okay?              “Yes Papa! What is happening? Mi kakeyi anan? Miya kawoka kano?”. Yoohan ya jerama papa tambayoyin yana zare jikinsa daga nasa tare da bin guards ɗinsa da ƴan sandan dake zagaye da su da kallon tuhuma suma.        Sake jawosa jikinsa papa yayi, batare daya bashi amsar ko ɗaya daga tambayoyin ba, ya shiga duba jikinsa sama da ƙasa kamar mai tunanin an masa wani abu. Sai kuma ya kama rigar shaddar jikinsa yana faɗin, “Yoohan minene wannan?”.       Wani irin luuuu da idanu Yoohan yayi tare da huro iska daga bakinsa. Cikin ƙosawa da abinda ke faruwa yace, “Papa kaya ne mana. Wai mi kukeyi anan wajen ne? Miya kawoka kano?”.              Cikin tsananin nuna ɓacin rai papa yace, “John! Yau kaine da kayan hausawa a jiki? Mike damun kanka da tunaninka?”.       Sake shiga wani takaicin shima Yoohan ɗin yayi, dan a take fuskarsa ta sake nuna fusata. Tayaya yana tambaya amma batare da an basa amsaba papa kuma na masa wasu tambayoyi mara kangado sai kace wani ƙaramin yaro. A tsawace ya kalli su Solomon da faɗin, “Mi kukazo yi anan nace?!!”.        Yanda ya daka tsawar basu Solomon kawai ba, hatta Emanuel da yaransa duk da suke ƴan sanda saida suka razana. Balle kuma ƴan anguwa da suka fara taruwa kallo. Gashi Yoohan yayi maganar ne da yare.        Solomon ne cikin rawar jiki data baki ya fara masa bayani,       “Sir! Dama mun zata ko wani abu mara ƙyaune ya sameka. Tunda muka tashi muka fahimci baka a cikin hotel ɗin. Gashi an duba ko ina amma babu alamarka. Ma'aikatan kuma duk sun tabbatar mana basuga fitarka ba, ga kuma wayoyinka mun samu baka fita dasu ba. To shine mukai tunanin ko anyi kidnapping ɗinka ne shine muka kira boss muka sanar masa.......”         “To da kuka kawosu nan, sune sukai kidnapping ɗin nawa kenan?”. Yoohan ya faɗa cikin katse Solomon.     Kasa bashi amsa Solomon yayi, dan harga ALLAH ba ƙaramin gulma da munafincin su baba malam sukai wajen papa ba akan gaba ɗaya sun janye ra'ayin Yoohan ɗinma, amma sunyi bakin ƙoƙarinsu suga tun a zuwan farko bai sake zuwa gidanba sai dai hakan ya gagara. Kuma jiya a yanda suka bar gidan yana cikin wani yanayi yasa sukai suspecting ɗin kosu baba malam ɗinne suka turo aka saceshi. Shiyyasa papa na isowa maganar gidan suka fara faɗa shiyyasa yace su kawosa....... ★★            Baba malam da Kubrah kusan a tare suka shiga falon. Shi ya fitone wajen Yoohan ɗin dan yanason su tattauna ta yanda ya kamata Yoohan ya fara neman ilimin dazai taimakamasa wajen bautar ALLAH. A tunaninsa zuwa lokacin ya kammala cin abincin da Nu'aymah taje kai masa. Dan rashin dawowar tata baisa sun zargi komaiba da ga shi har Umm. A tunaninsu ko bayan takai masan ta shiga sashen Hajjo ne ko kuma Addah.        Da sauri ya ƙarasa ga N'aymah daya hango ƙasa wanwar, ga kuma falon babu alamar Yoohan ɗin sai ƙamshin turarensa kawai. Tiren abincin data kawo yana a ajiye a inda ta ajiyesa.        “Ya ALLAH! K lafiya kuwa mamana? Mikikeyi kwance anan haka?!”. Baba malam ya faɗa yana kai hannu ga Nu'aymahn. Da sauri ya zabura dan jin jikinta yayi sanyi ƙalau ya saki. Yay azamar maida yatsunsa biyu wajen ƙofar hancinta. ‘tabbas bata numfashi’ ya ambata a zuciyarsa yana ɗagota gaba ɗayanta.      Hakan yayi dai-dai da ƙarasowar Kubrah da tun shigowar baba malam tana biye da shi, sai dai shi bai gantaba sai yanzun data ƙaraso garesu da dauri tana faɗin, “Abbah lafiya? Miya faru da ita ne?”.        Cikin tashin hankali baba malam yace, “Ban saniba nima Khadijah, kinga miƙo ruwa dan bata numfashi”.     A hanzarce ta ɗakko masa ruwan da Yoohan yasha ya bari, ya miƙa hannu ta tsiyaya masa. shafama Nu'aymah yay a fuska. sai dai ko motsi batayiba balle ai tunanun zata farko. Hankalin baba malam ne ya sake tashi matuƙa. Ya ɗago idanunsa da sukai jajur ya kalli Kubrah.         “Khadijah maza kiramin Ahmad ko malam ƙarami ko Omar. duk wanda kakaci karo dashi cemasa ya fiddo mota”.       Amsawa tai da to tana fita da sauri. Sai dai maimakon ta wuce aiken da akai mata saita samu waje ta laɓe abinta tana wani taɓe baki da sakin murmushin mugunta. Zuciyarta fes take akan halin da Nu'aymahr ke ciki. Ita ta mutu kota rayu hakan ba damuwarta bace a yanzu. Dan ita kaɗai tasan miyasa take bala'in jin zafin yarinyar.       Baba malam da baisan Kubrah bata tafi aikansa ba ya ɗakko Nu'aymah gaba ɗayanta ya fito. Da sauri Kubrah data hangosa ta sake maƙewa tana zaro ido waje. dan batai tunanin baba malam zai fito da Nu'aymah ba yanzun, a tunaninta ko saita kira ɗaya daga cikin wanda ya aiketan.     Oho shi hankalinsa ma bai kai gareta ba. Jikinsa na tsuma bakinsa na ambaton ALLAH ya nufi harabar gidan. cikin sa'a kuwa sai hakan yay dai-dai da fitowar malam ƙarami daga sashin su Kubrahn hannunsa ɗauke da leda da key ɗin mota.       “Abba lafiya? Miya sameta?”. Malam ƙarami ya faɗa a ruɗe yana nufo baba malam dake ɗauke da Nu'aymah.       Da sauri baba malam ya bashi amsa da, “Maza buɗemin mota malam ƙarami, yanzu ba lokacin sanin mafari bane ba”. Cikin sauri malam ƙarami ya cika umarnin baba malam. ya karasa ga motarsa ya buɗe. Baba malam na ƙoƙari sakata a ciki Kubrah ta ƙaraso wajen. Tamkar an kira Hajjo sai gata itama ta fito daga sashenta ita da Husnah da alama ma fita zatayi.       A rikice ta nufesu tana tambayar ba'asi. Dan taga yanda baba malam ya saka Nu'aymah a motar tamkar bata da rai. Babu yanda baba malam ya iya dole yayma Hajjo bayani a taƙaice. Kubrah na ƙoƙarin shiga motar dan a tafi da ita Hajjo ta tureta gefe ita ta shi. Yayinda Husna ta ƙirƙira cikin gidan da gudu tana ƙwalama Umm kira tana kuka. Dan ita a zatonta Nu'aymah kota mutune. Yarinyace ƙarama bata wuce 9years ba. Itace autar amaryar Abbah Musbahu.          Fara fitowar mutanen gidan saboda ihun Husna yay dai-dai da ficewar motar da aka sakata daga gidan. Sai dai suna fitowa idon Baba malam ya sauka akan su Yoohan. Da mamaki ya tsaida malam ƙarami dake ƙoƙarin hawa titin layin. buɗe motar yay ya fita yana faɗin, “Malam ƙarami kuje asibitin ina zuwa. da alama wajen nan babu lafiya dan kamar Yahya ne”.          Daga malam ƙarami har Hajjo dake baya riƙe da Nu'aymah tana faman jijjigata da tofa mata addu'a basu fahimcesa ba. Sai malam ƙaramin yabi umarni.                  Cikin nutsuwarsa ya ƙarasa garesu tare da yin sallama duk da alamarsu bai nuna na waɗanda ya dace yayma sallamarba. Sai bai saniba ko akwai musulmai a cikinsu. Ai ko cikin sa'a sai gashi wasu daga cikin ƴan sandan sun karɓa masa. Harda ma risinawa suna gaishesa dan darajar da ALLAH yay masa ta babban mutum kuma jagora.       Ya amsa musu ne idonsa akan Papa da sukema juna kallon sani. Kusan a tare papa da baba malam suka ambaci sunan juna.      “Pastor Goshpower!”. “Sheikh Sooraj Hashim!”.        Sai kuma kawai sukaga Papa ya kece da dariya yana tafa hannu. Ya sake nuna Baba malam yana faɗin, “Da gaske Sheikh Sooraj nake gani anan?”.        Kafin baba malam dake kallonsa fuskarsa babu yabo babu fallasa ya bashi amsa Solomon yace, “Sir! Ai shine mutumin da.......”       Malalacin kallon da Yoohan ke masane ya hanasa ƙarasawa, yay saurin duƙar da kansa ƙasa yana haɗiye sauran maganar.       Kallon Yoohan baba malam yayi. Sai kuma ya sauke wani lallausan murmushi. Cikin halin dattako irin na masu ilimi da sanin ya kamata yace, “Yahya ka sanshi ne?”.       Kai Yoohan ya jinjinama baba malam, kafin a hankali yace, “Mahaifina ne”.          Sosai alamar mamaki ya bayyana ga baba malam, dan fuskarsa ta nuna ƙuru-ƙuru. Yace, “Yahya da gaske?”.       Kafin Yoohan yay magana Papa da yay matuƙar tsuke fuska ya matso gaban baba malam ɗin yana faɗin, “Mizaisa ya maka ƙarya?”.       Kamar baba malam zaiyi magana sai kuma ya fasa. Ya sauke ajiyar zuciya a hankali yana sake dai-daita nutsuwarsa. Kusan sakanni goma kafin yace, “Okay! Alhmdllh. Inaga to muƙarasa ciki tunda yau gashi kazo gidana.....”         “Never!”. Papa ya faɗa cikin saurin katse baba malam ɗin.      Da sauri Yoohan yace, “Papa saboda mi?”.      Kallonsa papa yayi da tsananin ɓacin rai. Kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru ya sake maida kallonsa ga baba malam dake murmushi.         Baba malam yace, “Kayi haƙuri, dan kai yau sunanka baƙona. Ka cancanci na karramaka da masauki da abin ci da sha. Dan koba komai kazo ƙasata ne, yankina, gidana kuma”.        Tsaki papa ya ja. Tare da kallon d.p.o Emanuel yace, “D.p.o kama shi, inason sanin dalilin alaƙarsa da yarona”.       “What!!?” Yoohan ya faɗa a zabure yana ƙarasowa gaban papan. Cikin nuna fusata yace, “Papa mi kake shirin yi haka? Dammi zakasa a kamashi bayan ba'a cikin gidansa ka ganniba. Sannan ba tare da shi ka ganni ba”.         “Rufema mutane baki!!. Karna sake jin bakinka anan. Wannan wasane tsakanin manyan daji guda biyu. Ka shiga mota yanzun nan zamu koma Abuja da kai”.        “Babu inda zanje papa. Domin aikina ne ya kawoni nan. Banga kuma dalilin dazaisa na barshi ba akan dalili mara tushe. Ku kuma (ya faɗa yana nuna police ɗin) duk wanda yay gigin matsowa koda kusa da shi ne na rantse da ALLAH sai ya rasa aikinsa. Idan kunji ƙarya zaku iya gwada hakan kuma”.       Tashin hankaline ƙarara ya bayyana a fuskar d.p.o Emanuel. Dan shi kam an sakashi a tsaka mai wuya. Matsayin papaa a garesa ya wuce duk yanda mai karatu zaiyi hasashe. Sannan ɗansa Yoohan basai an faɗaba, yanada faɗa aji ga gwamnatin kowacce jaha saboda rawar da yake takawa akan harkar lafiya dama matsayinsa na babban likita da duniya gaba ɗaya ke ji da gani a yanzu. Dan tabbas yaron yana lokaci da lokacinsa.           “Yahya! Iyaye nada matuƙar daraja ga ɗa. Ka daina tsaurara harshenka ga mahaifinka kaji. Karka damu da tsakanina da shi, dan a yau a yanzu ya fini gaskiya tunda a wajena ya sameka. Ba'a wasa da iyaye. Dan haka karka sake maida masa magana kaji”. Baba malam ya faɗa idanunsa akan Yoohan dake ta faman haɗiyar zuciya da sauri-sauri.      Kai kawai ya ɗaga ma baba malam, dan zuciyar tazo wuya bazai iya magana ba. Ya watsama guards ɗinsa wani shegen kallo. Kafin ya raɓa papa da baba malam ya bar wajen batare da yayima kowa maganaba.              Papa da yasan minene fushin Yoohan yay saurin bin bayansa yana kiransa. Amma ko kallonsa baiyiba balle ya saka ran amsawa. Ya buɗe murfin motar a fusace ya shiga baya, shima Papa ɗayan gefen ya zagaya ya shiga yana cigaba da kiran sunan sa. Hakanne ya saka drivern sa da Solomon saurin shiga suma, sauran guards ɗinsa da su Emanuel da suka sami mafita suma suka nufi nasu motocin batare da suncema baba malam komaiba.              Nannauyan numfashi baba malam ya sauke lokacin da mitocin suka harba kan titi. Yayinda can ƙasan zuciyarsa ke mamaki da jinjina al'amarin UBANGIJI. ‘Yoohan ɗan Pastor Goshpower ne da gaske? Lallai UBANGIJI mai yin yanda yaso, a lokacin da yaso, ga kuma wanda yaso’. Baba malam ya faɗa a fili. Yasan tabbas UBANGIJI shike fidda rayayye a cikin matacce, ya kuma fidda matacce a cikin rayayye. Amma al'amarin akwai ɗunbin ban al'ajabi a cikinsa, dan yasan abubuwa masu yawa game da papa tun shuɗaɗen lokaci kafin yakai haka.        Da wannan tunanin baba malam ya koma cikin gidan, inda ya tadda duk jama'ar gidan sun fito sunata tararrabin abinda akace ya faru da Nu'aymah. Su Abban Abdallah ma shirin shiga mota suke zasubi bayansu asibitin.     Ganin baba malam ya sakasu dakatawa, duk suka nufesa hankali tashe suna tanbayar yaya Nu'aymahn.         Tausayinsu ne ya kamashi. dan haka cikin taushin murya ya kwantar musu da hankali, tare da sanar musu shima yanzu zai bisu. Basu zauna ɓata lokaciba suka ɗunguma a mota ɗaya Omar ya jasu, akabar su Umm a gida na binta da addu'a.        Yoohan da tunda suka tafi ya ƙi kula papa daketa so yayi magana yay kwance jikin kujera hannunsa dafe da goshinsa cike da tsananin takaicin abinda ya faru tsakaninsa da Nu'aymah yauma. Yarasa mike jan hankalinsa ga aikatama yarinyar nan wannan banzan ɗabi'ar?. Abinda ba halinsa ba amma yana ƙoƙarin ɗabi'antar da shi a gareta. Saima yaji na yau yafi masa zafi a rai fiye da na jiya.       Da sauri ya kwanto jikin papa saboda wata hajijiya-hajijiya dake neman kwasarsa. Sake rikicewa papa yayi. A matuƙar ruɗe ya shiga girgiza Yoohan kai kace gani yay baya numfashi.         Sosai takaici da hayaniyar papa ta sake rufe Yoohan ɗin, amma sai ya daure cikin taushin murya da sanyayata yace, “Papa Please relax. Ina lafiya fa”.        Da sauri ya rungumeshi yana sauke numfashi a jajjere. Su dai su Solo suna kallon ikon ALLAH daga gaba. A haka suka ƙarasa hotel ɗin da har yanzu akwai sauran yaran Ema... Da taimakon papa Yoohan ya fita, shine ya kamasa har ɗakin da yake. Su kuma su Solomon suka dakata wajen manager ɗin hotel ɗin suna musu bayani akan anga Yoohan ɗin su kwantar da hankalinsu.          Papa na zaune kusa da Yoohan dake kwance idanu a lumshe, hannunsa har yanzu dafe yake da kansa. Yama rasa wane kalar tunani ya dace yayi akan matsalarnan guda biyu. Alaƙalar Papa da Baba malam. Abinda ya aikatama Nu'aymah a karo na biyu. Buɗe idanunsa yay a hankali kan papa da yay shiru shima yana wani tunani can daban, sai da yay masa kusan kallon sakan goma kafin cikin nuna kulawa ya kamo hannunsa cikin nashi da faɗin, “Papa!”.        Firgigit ya dawo hankalinsa tare da kallonsa. Yoohan ya sake lumshe idanu ya buɗe a kansa. “Papa dama kasan malamin nan ne?”.      “Yoohan! Wannan tambayar taka bata da muhimmancin samun amsa. Kai ya kamata nasan minene alaƙarka da shi?”.        Kamar Yoohan ya faɗi ainahin gaskiya sai kuma wata zuciya ta gargaɗesa dayin hakan. Yunƙurawa yay ya tashi zaune sosai ya jingina da fuskar gadon. Hannunsa ya sake maidawa cikin na papansa, cikin kwantar da murya yace, “Papa akwai abinda nake buƙata a wajensa, shiyyasa na kwantar da kaina nake binsa a sannu harna cimma burina. Sai dai kuma gashi kai kazo cikin mintuna goma kacal kana shirin rusamin shiri na. Miyasa zaka biyema su Solomon da shirmensu? Ai koda suka sanar maka na ɓata ko tunanin inda za'a'a sameni kamata yayi ka jira harna dawo kaji ta bakina. Haba papa da girmanka a ƙasarnan amma kake abu tamkar wani mara.......”       Saurin katsesa papa yayi ta hanyar ɗaga masa hannu. hakanne ya saka Yoohan haɗiye sauran maganar tasa. Papa ya gyara zamansa sosai da cewa, “Naji nayi kuskure, amma kaima harda laifinka. Miyasa tun tuni baka sanarmin ba, bayan kasan niɗin mai baka goyon bayane akan kowanne irin business naka musamman a wannan yakin”.        “Nima naji nayi kuskure to. Amma ina da dalilin ɓoyewar ai. Da ace na sanar maka mi nake shirin yi zaka iya ɓatamin aiki dan kanada gaggawa papa. kai kafi son komai da zafi-zafi a lamarinka. Hakan kuma na taɗiyeka daga nasarorinka. Yanzu da ace bakazo ba da cikin satin nan zan kammala aikina. Amma yanzu kaga ka kawo min togaciya dan zai fara kokwanto a kaina. Kaga kenan saina sake sabon ginin da zai ƙara yarda dani hundred percent kamar farko”.      Cikin tsananin jin daɗi papa ya rungume Yoohan yana faɗin, “I am sorry my sweetheart, kai ɗinne ba'a gane kanka sai kaso. Yanzu dai na maka alƙawarin da kaina zan gyara abinda na ɓata a yau ɗinnan kaji”.         Ɗagowa Yoohan yay da sauri, yace, “Papa da gaske kakeyi?”.      “Ƙwarai kuwa my dear son”. Wani lallausan murmushi Yoohan ya saki najin daɗi. Dan ya fahimci lallai sai ya nunama papa akwai manufa a tafiyarsa da baba malam sannan zai samu nutsuwar samun damar fahimtar ilimin addinin islama da zai kare kansa anan gaba a wajensu dama duk wani dake a cikin ahalinsa da yasan zai kawo masa togaciya. Amma a yanzu yasan duk yunƙurin da zaiyi sai sun taɗesa saboda rauninsa na kasancewa sabo cikin addini mai ɗunbin haske irin musulinci. A yau kawai daya kasance a ciki jinsa yake tamkar sabon mutum. Tamkar darajarsa ta ƙaru. Duk wani nauyin zuciya da ƙunci da yakan tsinta kanshi a ciki a baya yau sai yaji tamkar ansa kwano an kwashesu tas.        Jikin papa ya sake lafewa tare da lumahe ido. Papa ma dake jin daɗin Yoohan ya fara ɗaukar huɗubarsa ya shiga shafa kansa cike da jin daɗi da annashuwa. Dan shima har zuciyarsa ta gama shirya masa babban aiki akan baba malam tsaf............✍ Tofa masu karatu. Yanzu za'a fara wasan😎 dan haka kumuje zuwa filin daga😉😱🚶🏻.        ZAFAFA BIYAR 2021 Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻. [5/20, 9:01 PM] Amina Mama: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*. No. 32 ............Tun isowarsu asibitin aka fara bama Nu'aymah dake a sume taimakon gaggawa. Sai dai harsu baba malam suka isa asibitin bata farfaɗo ba. Hakan sai ya sake ɗaga hankalinsu. musamman ma Hajjo dake ta faman sharɓar hawaye. Cike da kulawa baba malam ya zauna kusa da ita duk da kunyar ɗan fari dake tsakaninsu. Murya a tausashe da nuna ɗunbin kulawa da ladabi ya fara lallashinta da faɗa mata kalamai masu taushi da nutsuwa irin na masu ilimi. Ya nuna mata koda rasa Nu'aymah sukayi su zama masu haƙuri da godema ALLAH. Dan lokacin da ya basu ita baiyi shawara da suba. A yansu kuwa idan ya karɓeta ya fisu bukatarta ne.      Haka ya cigaba da mata nasiha harta samu nutsuwa tai shiru. Abba Musbahu yazo gabanta ya durƙusa tare da saka handkherchief ya share mata hawayen.      Ana haka Doctor ya fito daga ɗakin da aka sanya Nu'aymahn. Ya buƙaci ganin ɗaya daga cikinsu cikin nuna girmamawa a garesu. Abban Abdallah da Abban su Adawiya ne suka bisa office. Dan baba malam ya nuna kawaicin nasa da ya saba kamar ko yaushe. Amma zuciyarsa cike take da tsoro da rauni. Yana ta dai ƙoƙarin danneta ne da ambaton ALLAH wajen ƙarfafa imaninsa.        A office ɗin likita kuwa ya nutsu ne wajen rubuce-rubuce a wata takarda kafin ya maida hankalinsa gasu Abbah.        “ALLAH ya gafarta malam zan fara da muku albishir ɗin farfaɗowarta. Sai dai kuma kamar yanda kuka sani raunin dake a cikin ƙwaƙwalwarta shine ya motsa mata. Kuma gaskiya a bincikenmu yarinyarnan tana matuƙar buƙatar son ganin babban likita. Idan ba hakaba a koda yaushe zata iya fuskantar gogewar komai na ƙwaƙwalwar ta. saboda tana ƙara girma ciwon na daɗa faɗi. Musamman ma daya kasance kamar tana sakama kanta abubuwa masu nauyi a cikin rai. A duk kuma lokacin data shiga ƙunci ciwon na mata kuɗa a cikin kanta, ba dan ma tana samun kulawa da kuma addu'oi ba da gaskiya bana zaton yarinyarnan zata kai wannan shekarun batare data tsinci kanta a ciwon hauka ba. Duk da komai na ALLAH ne, babu wani bawa daya isa canja ƙaddarar wani bawa daga yanda tazo a littafinsa. Amma a wannan karon ayi himmar sadata da likitan daya dace da matsalarta, munan taimako kawai muke bata na dakatar da raɗaɗin a gareta a lokacin daya taso. Amma matsalarta sake hauhawa takeyi gaskiya”.        Su Abba da duk jikinsu yay sanyi sukaima Doctor godiya sosai. Tare da tabbatar masa insha ALLAHU a wannan karon zasuyi abinda ya dace.      Yaji daɗin hakan sosai. Ya sake ɗan musu wasu bayanan da suka dace akan yanayin kula da Nu'aymahn kafin ALLAH yasa a dace da samun Doctor ɗin daya faɗa. Dan ya basu note dazai taimaka musu samun ganin makusancin likitan da lokaci-lokaci yake shigowa cikin kano. Baya kuma duba marasa lafiya a ko ina sai a General hospital. Dan haka ya basu abinda zai taimaka musu ganawa da wata likita dake aiki a General hospital ɗin, wadda yake da tabbatacin ta hanyarta zasu iya ganin Doctorn.      Godiya sukai masa sosai, sannan suka fito. Sai dai basu ma su baba malam bayanin komaiba, a ƙoƙarinsu nason yin wani hoɓɓasa akan jinin yayan nasu da a kullum hidimarsa ke ƙarewa a kan su da nasu iyalin. Suma wannan karon sunason nuna tasu bajintar akan ɗaya daga cikin jininsa guda biyu da ALLAH ya bashi. ________★★           Ganin lokacin sallar la'adar ya gabato Yoohan ya buƙaci kaɗaicewa dan ya huta. Hakanne ya saka papa fita ya barsa shima ya nufi ɗakin da aka kama masa.       Yoohan ya ɗan sauke ajiyar zuciya yana miƙewa. Zuwa yay ya sakama ƙofar ɗakin key. Kafin ya nufi bayi yayo alwala kamar yanda baba malam ya koya masa. Duk da zuciyarsa na kwaɗayin zuwa massallaci yay salla cikin jam'i kamar yanda suka gabatar ɗazun a massallacin juma'a haka ya haƙura ya daure yin tasa shi kaɗai a cikin ɗakin kamar yanda aka koyar da shi.      Bayan ya idar da sallar a tsanake yay addu'a gwargwadon abinda ALLAH ya hore masa. Waya ya jawo yay kiran baba malam. Cikin sa'a kuwa bugu biyu aka ɗaka. Sassanyar ajiyar zuciya ya sauke wadda har baba malam ya jiyota.         “Banyi zaton zaka ɗagaminba Uncle. Nazata zakayi fushi dani bisa kuskuren papa”.          Baba malam da fitowarsa kenan daga massallacin cikin asibiti sun idar da salla kiran ya shigo masa yay sassanyan murmushi, ƙaunar Yoohan ɗin da ƙyawawan ɗabi'unsa na sake dulmiyasa a ƙaunar yaron. Cikin kulawa yace, “Haba Yahya! Mizaisa nayi fushi da kai? Ai koshi bazanyi fushi da shiba dan ya fini gaskiya. Da farko ina fatan dai ka gabatar da sallar la'asar. Na biyu kuma ina fatan babu wata matsala tsakaninka da mahaifinka a dalilin ganinka da yay a wajena?”.        Lumshe idanu Yoohan yay a hankali yana jingina bayansa da kujera, cikin so da ƙaunar baba malam dake ratsashi shima yace, “Alhamdulillahi Uncle. Yanzun nan na idar da salla, sai dai banje massallaci ba, ina fatan hakan ba laifi baneba. Dan nayi hakanne saboda ahalina, banason su fahimci ni musulmi ne tun yanzu dan zasubi hanyoyi da dama wajen kaini ƙasa. Amma idan na sami wadataccen ilimin addini musulinci duk ta inda suka ɓullo zan kare kaina”.           Baba malam dake murmushi ya sauke ajiyar zuciya. “Tunaninka mai ƙyau ne Yahya. Sai dai salla cikin jam'i tanada matuƙar muhimmanci, dan haka kar kayi sakaci da samun ladan dake cikin jam'i kaji”.        “Zan kiyaye Uncle”. “Alhamdulillahi haka ake so. Mahaifinka fa?”.         “Karka damu da shi Uncle. haka yake da zafi, amma da an fahimtar da shi yanada saurin fahimta. Munyi magana da shi ya kuma fahimceni, kafin ma ya wuce zai shigo wajenka yacemin”.          Hakan ya bama baba malam mamaki matuƙa. Amma sai bai nunama Yoohan ba ya amsa masa kawai. Sannan sukai sallama.          Lokacin da Yoohan ke waya da baba malam a can papa ma yana ɗakinsa suna waya da Uncles ɗin Yoohan ɗin su Uncle Godwin. Ba akan komai suke wayarba sai akan baba malam. Kamar yanda papa ya girgiza da ganin Yoohan da farko haka suma suka girgiza dajin Yoohan a wajen baba malam. amma daga baya sai bayanin da Yoohan yayma papa ɗin yaɗan sanyaya musu rai.      Uncle Mike yay wata dariyar mugunta yana faɗin, “Wannan ɗan nakafa shegen kansane, inaga akwai aikin da yakema turawan nan ta ƙarƙashin ƙasa shiyyasa kullum bai damuwa da lamarin kowa sai wannan aikin nasa. A da ba ƙaramin haushi yake baniba akan hakan, amma jin wannan maganar ta yau sai naji ƙaunarsa da son haɗa tafiya da shi. Sai dai matsalar ɗaya ce yaron yanada taurin kai, nasan bazai taɓa yarda musan cikinsa gaba ɗaya ba. Amma ni a ganina mizai hana muma muyi namu aikin akan wannan hausa man ɗin, dan fa multi millions ne. Kawai dai baya nunawa ne”.          Papa ya kwashe da wata dariya, kafin yace, “Mike! tunaninmu ɗaya, dan haka ku bari sai na shigo Abuja mu tattauna da ƙyau. Yanzu dai matakin farko zanbi shawarar Yoohan zanje har gida na bashi haƙuri. Daga haka na ƙulla alaƙa mai ƙarfi da shi. Sauran bayani kuma sai mun zauna a tebirin shawara”.     Duk sunyi na'am da hakan suma. Dan haka yay musu sallama ya kashe wayar cike da zumuɗi a ransa. Kaɗan-kaɗan sai ya ƙyalƙyale da dariya. Dan gaba ɗaya zuciyarsa ta gama tsara masa yanda komai zai kasance. ______________★★          Bayan Baba malam sun shiga sun duba Nu'aymah dake barci suka bar Hajjo da Abba Musbahu a asibitin. Koda suka iso gidan sai su Umm suka shirya su kuma suka tafi duba Nu'aymah. Wanka yayi ya zauna a falonsa yaci abincin da Umm ta shirya masa kafin su wuce. Abincin kawai yake ci a zahiri, sai dai zuciyarsa sam bata tare da duniyar mutane. Yayi zurfi matuƙa gaya a tunanin Pastor Goshpower (Papa). Ba komai ya kaisa ga tunaninba kuwa sai mamakin dama Papa nada babban ɗa a duniya kamar Yoohan? Ga shi dai a zahiri akwai kamanni tsakaninsu, sai dai baisan miyasa zuciyarsa ke kawo masa wani al'amari mai kama da kokwanto a cikin zuciyaba. Musamman da zuciyar tasa ke tariyo masa wani shuɗaɗɗen al'amari daya faru a shekarun baya tsakaninsa da Papan.        Haka yayta saƙawa da kwancewa har lokaci yaja bai farga ba. Sai da Abban Abdallah ya shigo dubasa sannan ya fahimci yayi zurfi sosai a tunani ashe. Alwala yayi suka fice massallaci dan lokacin sallar magriba ya gabato     Suna fitowa su Umm na dawowa gidan. tambayar jikin Nu'aymah sukayi. Suka sanar musu har yanzu tana barci, batama san sunje ba balle tahowarsu.         Baba malam yabi Umm da kallo harta shige. tausayinta mai tsanani ne ke sake shigarsa. Tanada haƙuri da kawaici matuƙa, shiyyasa yake tsananin ƙaunarta fiye da zaton mai hasashe. Yanzu haka inba shi daya gama sanin kayarsa ciki da bai ba bazaka taɓa fahimtar tanada damuwa ba a fuskarta. Ta dake ta shanye komai, baka ganin komai akan fuskarta sai tsananin jarumta da tarin haƙuri da juriya.      Haka ya tafi massallaci da wannan tunanin na Umm.          Bayan idar da sallar isha'i suna shirin zaman karatu kamar yanda suka saba ɗaya daga cikin ƴan agajin massallacin ya shigo ya sanar masa cewar yayi baƙi.     Jimm yayi alamar tunanin baƙi daga ina a wannan lokacin? Bai gama kaiwa ƙarshe ba ya hango Yoohan dake ƙoƙarin shigowa massallacin. Bai tashi ba, sai ya jira harya ƙaraso inda suke. Yoohan da kallo ɗaya zakai masa ka fahimci damuwa da rashin walwalarsa kamar ko yaushe ya ɗan bama na kusa da shi hannu sukai musabaha kafin ya ƙarasa inda baba malam ɗin yake. Cike da girmamawa ya risina ya gaishesa. Amma sai baba malam ɗin ya kamo hannunsa cikin nasa sukai musabaha kamar kowa. Cike da jin nauyi Yoohan yay masa bayanin tare yake da baƙi, wannan ya saka baba malam miƙewa bayan ya bama ɗalibansa haƙuri ya barsu da Abbansu Abdallah shi kuma suka fito.        Duk da dai yayi mamakin ganin papa ne sai baice komaiba. Da kansa yay musu iso gidan saukar baƙinsu. Sannan ya kira Umm ta bada abinda ke akwai a gidan cikin su Omar wani ya kawo.          Papa dake ta waya tun ɗazun ya ajiye yana kallon baba malam da murmushi, shima bai gazaba wajen maida masa murtani. A ƙasan ransa kuwa yana neman tsarin ALLAH da ga kowanne irin sharri papan ke tare da shi ko yake shirin ƙullawa. Duk da shi mutum ne mai ƙyautatama mutane zato zuciyarsa ta kasa ƙyautata zaton akan papa, dan shi shaidane akan sanin papa bayahude ne na gaske, sai dai bai saniba ko yanzu ya canja daga yanda ya sanshi a da ɗin.          Hannu ya bashi suka gaisa, hakan yay dai-dai da shigowar Omar ɗauke da basket da Umm ta shiryo abincin motsa baki. Sai da ya gaida Papan, suka gaisa da Yoohan da alamar sanayya tsakaninsu sannan ya fice. Papa ya gyara zamansa yana wani ɗan basarwa, fuskarsa da murmushi har yanzu ya duba baba malam da faɗin, “Kayi haƙuri da kuskurena na ɗazun, ina fatan zaka dubesa akan rashin sani na aikata. Bansan alaƙarka da yarona mai daraja bace irin haka sai bayan mun barka ne yaymin bayanin da har na fahimta, ina fatan zakamin afuwa”.       Sosai mamaki ya kama baba malam, dan duk zatonsa Yoohan ya ma mahaifinsa bayanin ya musulunta ne. dan haka ya ɗan dubi Yoohan ɗin. Da sauri Yoohan ya girgiza masa kai yanda papa bazai fahimtaba, hakanne ya saka baba malam fahimtar akwai abinda Yoohan ya sanarma mahaifinsa daban kenan. Sai kawai ya murmusa abinsa ya fuskanci papan shima.        “Karka damu komai ya wuce. Dama kuma ni ban ɗaukesa wani abuba. A inda ya faru anan na zubar da shi, nima ina fatan kaimin afuwa ka kuma fahimci alkairine ya haɗani da Yahya ba sharriba. Sanin shi wanene kuma bazaisa na taɓa cutar da shi ba insha ALLAHU. Saɓanin dake tsakanina da kai kuma bana fatan ya zama sanadin ɓata alaƙata da shi, dan sanin kai ne mahaifinsa bazai canja komai ba daga yanda na ɗaukesa a raina”.        “Naji daɗin haka, na kuma gode sosai da wannan girmamawa”. Papa ya faɗa yana sake faɗaɗa fuskarsa da murmushin mugunta.      Daga haka dai suka ɗan taɓa hirar da bawani tsaho taiba, shi dai ma Yoohan ba saka musu baki ya keba, yama maida dukkan hankalinsa ne ga wayarsa kamar baya falon. Kusan awarsu ɗaya da rabi sukai masa sallama suka fito inda su Solomon suke. Sai da baba malam yaga barin motocinsu anguwar sannan ya shiga cikin gida ransa taf da wasiwasi akan wannan ziyara ta Pastor Goshpower, amma sai ya bar abinsa a zuciya bai faɗama kowa ba, ya ma maida hankalinsa wajen kwantarma matarsa hankali akan damuwar ciwan ɗiyarsu. WASHE GARI.           Washe gari papa ya matsa akan sai Yoohan ya bisa sun koma Abuja. Badan yaso hakanba ya amince zai bisa, dan dama yau ɗinne zai kammala abinda ya kawosa kanon. Yaso komawa wajen baba malam dansu tattauna game da neman iliminsa amma papa ya tsare ko ina ya hanashi matsawa ko nan da can. Asibiti ma binsa yay sukaje tare, ya kuma zauna a office ɗinsa har sai da ya kammala komai suka fito.       Da ga asibitin airport suka tafi kai tsaye, sai da jirginsu ya ɗaga sannan guards ɗinsa suka ɗauki hanya suma a motocin.       Baba malam na asibiti wajen duba jikin Nu'aymah da jikinta Alhmdllh saƙo ya shigo masa. Buɗewa yay ya duba ganin Yoohan ne. Murmushi baba malam yayi saboda ganin abinda saƙon ya ƙunsa, a ransa kuwa yana tsananin tausayi da ƙaunar Yoohan, insha ALLAH yayi alƙawarin zai taimaki yaron nan har ya zama HASKEn da zai zama HASKE ga waɗansu.     Ajiye wayar yay ya maida hankali ga Nu'aymah da Hajjo take lallaɓawa taci abinci amma sai shagwaɓa take ita ta ƙoshi. Ya ɗan murmusa tare da kamo hannunta cikin nashi. “Mamana daure kici ko kaɗanne kinji, inba hakaba fa kinsan Doctor yace allura zai miki, idan kuma kin fison allurar to sai a kirashi kawai”.      Da sauri ta shiga girgiza kanta idanunta cike da ƙwalla. “Abba dan ALLAH a'a banaso”.       “To ki daure kici abincin sai kisha magani ki kwanta ki huta. Kinga kince dama kanki na ciwo har yanzu, Doctor kuma yace kina buƙatar hutune sosai”.       Kanta ta sake jinjina masa. Hajjo da batace musu komaiba ta miƙama baba malam abincin. Babu musu ya amsa ya fara bata da kansa. Batafi spoon huɗu ba su Ahmad suka shigo ɗakin bayan sunyi sallama an basu izini. Ba Nu'aymah kawai ba hatta Hajjo da baba malam da ɗunbin mamaki suke kallon wanda ya shigo tare da su Ahmad ɗin. Ba kowa bane face Nasir jikan yayar Hajjo.      Babu kunya idonsa fes akan Nu'aymah da mamakin ganin nasa ya sakata masa kallo mai nisan zango. Hajjo ce ta katse su da faɗin, “Naseru yaushe a gari? Inji maƙi baƙo?”.           Goshinsa yaɗan sosa najin kunyar kallon da baba malam ke masa. Kafin yace, “Hajjo yanzun nan muka iso”.        “Kuka iso? To kai da wa kuma?”. Kansa tsaye yace, “Rufaidah”.       Baba malam da tun gaisuwar daya amsa musu baice komai ba sai yanzu yace, “Lafiya dai ko Naser? Yau ka tuna damu a duniya”.         “Ayi haƙuri Kawu, ni ɗin mai laifine kam, mun tahone saboda ga biki nata gabatowa, ganin mun sami hutun makaranta mu duka sai kawai nace bara mu taho maɗan huta ai”.       “Oh to masha ALLAHU, ALLAH yayi jagora to”.      A tare suka amsa da amin. Nu'aymah dai bata tanka ba, tama ɗauke kanta tamkar batasan mi akeyiba. Sai da Naser ya tambayeta yaya jikin sannan ta gaidashi batare data kallesanba yanzun ma. Shiko yanata so su sake haɗa ido ko zaiji ɗan sanyi a ransa da ruhinsa.      Miƙewa baba malam yayi yana faɗin, “To ni bara naje gida hajjo, dan ina saka ran zuwan wasu baƙi ɗan anjima kaɗan idan ALLAH ya kaimu. Idan sun wuce insha ALLAHU zan dawo muji ko zasu bamu sallama, banason zama asibitin nan sam”.       Amsa masa hajjo tayi tare da binsa da addu'a. Nu'aymah ma ma dasu Ahmad sukai masa sallama ya fice. Hajjo ce ta sake cigaba da bama Aymah abincin, badan yana mata daɗi ba take amsa, sai dai mayataccen kallon da Naser ke mata duk ya sake takureta matuƙa, sannan ya tuno mata da wasu shuɗaɗɗun abubuwa dake tdakaninsu a lokacin ƙuruciyarta, hakan yasa taketa cuno baki gaba da ɓata fuska duk da ƙasan ranta cike yake da mamakin ganin nasa ya dawo bayan barinsu na tsahon shekaru da yayi akanta.           Idan bata manta ba shekara kusan takwas kenan rabonsa da kano. Dan tunda tace masa ita Yah Abdallah ne zaɓinta yay zuciya saboda goyon baya da Hajjo ta bama Abdallah a wancan lokacin. Anyi bukukuwa kashi-kashi a gidansu shi kaɗai ne baya zuwa sam.     Ta ɗan sake satar kallonsa da jijjina ƙyawun daya ƙara da cikar kamala tamkar ba Yah Naser ɗin data sani ba a shekarun baya. Kallo ɗaya zaka masa ka fahimci yanzu kam kuɗi sun zauna a garesa da hutu, dan sai ɗaukar ido yake kamar gasashshiyar kazar gidan gona.     *_Naser yaro ne wajen Alhaji Kabeer Usama dake a garin katsina. Jikane ga Yayar hajjo da suke uwa ɗaya uba ɗaya, dan aurene ya kaita katsina ta zuba zuri'a kuma a can mai albarka. Ita kaɗai kuma ta ragema hajjo a yanzun, shiyyasa take ɗaukarta tamkar uwa. Naseer ya zauna a gidan su Nu'aymah sosai, dan rashin yara a gidan lokacin da su Abdallah sukai Accident yasa hajjo ɗakkosa. A wajensu yay primary ɗinsa har secondary. Jami'a ce kawai ta maidashi garin jos. Yaso nu'aymah shima tun tana ƙarama, dan lokacin takara suka dingayi da Abdallah a kanta duk da kowa bai furta ba saboda ƙuruciya. To sai kuma yazam sanda suka furta ɗin ya zam lokaci guda, sai dai Abdallah ya riga Naser. Dama kuma ya fisa nuna damuwa da Nu'aymah. Hakan ya haddasa rigima sosai tsakaninsu, da Hajjo taga lamarin zai girmama ne tai musu shari'a a tsakani da shaidar cewar Abdallah ya riga Naser ɗin. Wannan shine sanadin yin zuciya ya tattara komansa yabar kano ya koma gidansu. Bai kuma sake zuwa ba sai yau ɗin nan da suka gansa tsulum. Har yanzu kuma baiyi aure ba._*..........✍       To ga dai Naser tsohon masoyin Nu'aymah a kano bayan gudun hijira na shkara takwas da yayi. Ko da wane shiri ya dawo yanzun kuma? Dan da alama kam akwai motsawar tsohon tsumi tattare da shi dama ita kanta, sai mu cigaba da binsa muji YAYA TAKE NE?!!🤗. ZAFAFA BIYAR 2021 Hafsat miss xoxo🥰 KIBIYAR AJALI......!       (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗              Mamu gee🥰 MIN ƘALB!!😋🤗         Hafsat rano🥰 ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗         Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗          Bilyn Abdull🥰 SARAN ƁOYE🤗😋     Duka akan farashi mai rahusar gaske. Kamar haka👇🏻💃🏻 Ɗaya___300 Biyu____400 Uku_____450 Huɗu____500 Biyar_____700 Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇 ACCOUNT NO 0812652655 ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO BANK NAME: ACCESS BANK. saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇 0903 234 5899 IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇   09033181070 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍 ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.