PAID PAGE 1️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Tsammanin dawowarsa da kuma tsumayi na shiga sabuwar rayuwa da sabon gida ya hanani runtsawa. Da zarar na rufe idon sai na ji wani yanayi na dabam, mafi munin tunani shi ne na Zafeer, a wane hali yake ciki a yanzu? Ya rayuwa zata kasance masa a yanzu da lokacin da ya tabbatar da rabuwarmu? A take wata zuciyar ta raya min be kamata na yi tunanin wani namijin da ba muharramina ba a karkashin inuwar wani namiji da yanzu aljannata take karkashin takun kafarsa. Forcing kaina na fara yi ina son bachi ya dauke ni, amman ya ki ya ba ni hadin kai, tun ina jin abun normal har na fara jin tsoro daman bana son kasancewar ina kadai a guri, kowa ma ya san wannan a gidanmu. Saukowa na yi a hankali ina kara rufe jikina da mayafin da Hafiz ya yaye min, na fara taka tile din mai tsananin sanyin da zan iya cewa na ac dake dakin ne, bakunta bata bar ni na karasa kofar da sauri ba, kamar wadda zata yi sata haka na isa gurin na rika kofar dakin na bude kadan na leka falon da aka kawata da kayan alatu, sai dai ban tsaya tantance abubuwan cikin sitting room din ba, domin ba su ne a gabana ba. Numfashin da nake ta hanci ne ya dawo yana fita ta baki saboda tsoro da kuma mamakin a ina Hafiz ya tafi? Na juyo a hankali na rufe kofar na dawo saman gadona na hau, na janyo filo na dora daga tsakiya, fitar numfashina na kara ta'azzara saboda tsoron da ya nufato ni. Rumgume pillow na yi sosai ina kallon agogon dake dakin, tun ina kirga dakika har na fara da mintu, awanni suka biyo baya. Shiru babu Hafiz babu labarinsa sai da, sanyin saukar hawaye na ji a fuskata sun gangara zuwa kunne kasancewar ina kwance ne. Ba ni waya balle na kira shi na tunatar da shi idan ya manta da ni, domin tsoro na neman haddasa min tashin hankali a cikin daren Amarya ci na. “Ko dai ya manta ya auro ni? Ko kuma be gama rarrashinta ba har yanzu? Ko kuma wani abun ya faru?” Na kasa samun amsar duka tambayoyina ukun, natsuwa kuma tace min yau ba ni tare da ke Noor, tsoro da kadaice ya maye min gurbinta, na yakure guri daya kamar marainiya. Ina kwance shiru akan gadon har karfe hudu na Asuba, misalin Biyar daidai na ji karar murda kofar an turo, tsoro ya saka ni kasa motsawa bana son na yi arba da abun da zai daga min hankali. “Noor Amarya... A gafarce ni dan Allah ko kin yi bachi...” Jin muryar Hafiz ya zabtare rabin tsoron dake tare da ni, cikin hikima da azanci na sauke ajiyar zuciya, na yi hanzarin rufe idona dake cike da kwalla domin na fahimci yana kokarin zagayo ne ta gurin da fuskata take facing. “Bachi kike yi” Ya tambaya yana taba ni, ni kuma ban motsa ba har sai da ya fara shafa fuskata yana girgiza ni a hankali, na bude idon sai dai ban iya tare hawayen idona ba har sai da suka zuba, sai da na yi hanzarin kai hannuna na share. “Amarya tashi asuba ta yi...” Ya riko hannuna yana murza yatsun a hankali, jiki ya dan fara rawa ina jin kamar babu dadi, ba kuma dan ba a taba rika hannun nawa ba, sai dan nashi rikon nake jinsa dabam wata kila saboda ina kallonsa a wani yanayi ne na dabam. “Taso mu yi alwala” Kamin na yi wani yunkuri har ya fara kokarin sauko da ni kan gado, ganin hakan ya saka ni saurin saukowa da kafafuwana na mike tsaye, sai ya yaye veil din da na lulluba da shi ya aje min kan gado, ya rika hannuna zuwa bandakin. Tsayawa na yi sai da ya fara alwala sannan ya juyo ya kalleni. “Shigo mana ki yi alwala” Na fara takawa kamar bana son isa gurin. Shi kuma sai ya fita ya ja min kofar bandakin. Sai da na gama kallon bandakin da ya banbanta da na gidanmu a komai sannan na tunna gurin da na ga ya taba ruwa ya zo na fara wanke baki, sai da na yi rabin alwala na ji ina jin fitsari. Na nufi bathtub na yi tsarin a ciki sannan na dawo na sake yin wata alwalar. Ko da na bude kofar na dakin na fito na same shi yana sallah, na yi zaton ko zai jira ne sai na fito mu yi sallah a tare kamar yadda nake gani a fina fina wasu ma'autan na yi. Mayafina na dauka na lulluba sannan na tsaya kan sallayar dake shimfide a gafensa, na kabbarta sallah na fara. Bayan na sallame muka hada ido sai ya sakar min murmushi ya miko hannunsa ya kama hannuna ya rike. “Good Morning, Amarya a gafarce ni, na miki laifi biyu” Na sauke kaina kasa haka nan kawai nake jin kunya abun da ba halina ba. Kamar ya san tambayar kaina nake laifin a zuciyata sai na ji ya ce. “Na farko na manta, ban aje miki kayan bachi ko na sallah ba, gaba daya hankalina na dauku Wallahi na manta sam, abu na biyu kuma wanda shi ya fi kowane laifi shi ne na tafiya na bar tsaleliyar amarya mai kyau irinki ta kwana ita kadai a gafarce dan Allah” Na yi shiru kaina na kasa sai saurarensa nake. “Na je na rarrashi Yayarki ne, tun abun yana kuka zallah har aljannunta suka tashi” Na kalleshi da sauri cikin wani irin tsoro, domin idan akwai mai tsoron aljannu a dubiyar nan to a bayana yake. “Aljannu?” “Eh Wallahi ni ma ban taba sani tana da su ba sai jiya, karki so ganin yadda muka kwana a wahale sai da na riketa, da zarar na motsa sai ta fara ihu sai asuba ta samu ta yi bachin kirki, na tsorata sosai saboda cikin dake jikinta” “Subhanallahi, Allah ya bata lafiya” “Ameen” Na ji ya sunbanci hannuna yana murmushi. “Abubuwan da ya kamata mu gabatar a darenmu farko na angonci ni da ke ba mu samu yi ba, wata kila sai yau...” Ya kwantar da ni kafadarsa yana shafa fuska mai soft face dina. “Wata kila kin kwana a cikin tsoro a gidan da baki saba ba ko Amaryata” Na yi shiru ban ce komai ba. Daga ni daga kafadarsa ya tashi na nufi gurin da wasu ledodi suke aje a jiye tun jiya ya dauko yana fadin. “Wata kila kazar nan ta buga ma, madadin li bude ki ci ko bana kusa na ki ne fa” A nan ma ban ji zan iya cewa komai ba saboda haka na yi shiru ina kallon ledodin da aka fito da su daga restaurant din mutumen da ya zama silar haduwa ta da mijina a yanzu. Ya bude kazar da kabejin ya fara bugawa yana wari kaza ce har uku da yoghurt sai wani kalar lemu mai kamar giya. Ya ci kazar kadan ya aje ya dauki tissue ya goge hannunsa. “Ba zan bari ki ci wannan ba zata iya lalata miki ciki, sai dai anjima na siyo miki wata” Nan ma ban ce komai ba, har ya mike tsaye ya kwashe ledodin ya nufi kofa. “Bari na saka lemun yayi sanyi” Na bishi da kallo har sai da ya fice sannan na juyo na ina jin idona suna cika da hawayen da ban san na minene ba. Ina jin motsin taba kofar dakin na yi hanzarin share hawayena gabana yana faduwa sosai. “Amarya... Let go back to sleep kamin rana ta yi masu zuwa ganin amarya su fara zuwa” Ya rada min a kunne sannan ya kai hannunsa ya riko fuskata ya juyo da ni na fuskance shi, sai dai ban yarda na kalli idonsa har ya mikar da ni tsaye, muka nufi gadon sai da ya fara zaunar da ni sannan ya zauna kusa da ni sosai ya sumbanci kumatuna na dama, a na hagun ne muka ji an bugar kofar falo. Ya kalleni da dan mamaki sannan ya sake ni ya mike tsaye. “Ina zuwa” Da ido na bishi har ya fice babu jimawa na ji hayaniyar yara da na tabbatar nasa ne domin garin be karasa wayewa balle na yi zaton ko na masu zuwa ganin amarya ne ko na makota. “Abba Abba Abba” Na ji suke ta fada, hakan kuma ya faranta min dai domin bana sha'awar kwantawa a gado daya da Hafiz, kamar yadda bana sha'awar yadda yake taba ni ko kuma sumbantar da ya fara a yanzu. Cikin dakin ya dawo yana rike da hannayensu su uku duka mata babbar ta fi kama da shi sai kuma karamar da ta zuba shagwaba. Muna hada ido da su na sakar musu murmushi ta biyun ta mayar min babbar kuma kallona kawai take. “To ku gaishe ta mana” Ya fada musu sannan ya zauna ya dora su a tsakiyarmu yana shafa kansu fuskarsa cike da annuri kana gani ka san yana jinsu sosai a ransa. “Ina kwana” Babbar ta fada sai na amsa murya a dakishe, ta biyun ma ta gaishe ni har ta ukun. “Anty zaku rika kiranta daga yau kun ji?” Suka daga masa kai, sai ya sumbance su yana murmushi ya kalleni. “Wannan ce babbar sunanta Walida, ta biyun kuma Ikram sai kuma Haulat ita ce karama a yanzu” Na yi murmushin dole ina kallonsu domin jina nake a takure. Kamar ya fahimci haka sai na ji ya ce. “Noor baki son magana, kamar ba ke ba yadda Kareem yake ba ni labarinki sai na ganki a dabam, ko da yake.... Zaki saba zaki sake mana nan gaba” Na yi murmushin yaƙe ina kallon kasa. “Abba Momy tace ka hadawa Haulat breakfast ita bata jindadi, Haulat kuma ta fara kukan yunwa” Na ji babbar tana fada, sai ya daga Haulat din ya dora a cinyarsa. “Haulatu kin fara jin yunwa?” Ta daga kai. “Na san halinki ai sarkin cin abinci, daman ke kina rigan kowa karyawa acici” Kannen suka saka dariya. Sai ya kalleni a yayin da ya mike tsaye yana dauke da karamar. “Anty zo muje ki gaishe da yayarki ko ki yi mata ya jiki” Na mike tsaye na dauki mayafina na saka sai Ikram ta kama hannuna hakan ya saka na dan ji kwarin guiwar tafiyar, yana gaba da yaransa biyu ni kuma ina daga baya tare da Ikram, har muka shiga bangaren matarsa wanda ya kasance iri daya da na nawa bangaren sai dai nata furnitures din da komai ya fi nawa kyau, a kudi kuma kana kallo zaka san nata ya fi nawa tsada nesa ba kusa ba. Hoton Hafiz da na yaranta da nata a naka manne a falon, wani gurin sun yi a tare wani gurin ita da yara wani gurin kuma shi da yara dayan kuma yaran ne su kadai aka yi ma hoton. Uwar daka muka shiga wato bedroom muka shiga, shi ya fara sallama sannan ni ma na yi na shiga. Zaune na hangota kafafuwanta a kasa, sam bata yi kama da mai aljannu ba, haka kuma bata yi yanayi da marar lafiya ba, sai dai tsoron aljannu ko mutane masu aljannu da nake ya hanani karasa kusa da ita, sai na zauna a kujerar dake kusa da kofar ina kallonta, shi kuma ya karasa ya zauna kusa da ita. “Ina kwana?” Ta yi min murmushi kamar yadda ta saba sannan ta amsa. “Kin kwana lafiya Amarya? Ya bakunta?” “Alhamdullahi” “Madam ya jikin?” Ta kalleshi tana wani irin lumshe ido ta bude kamar karuwa. “Alhamdullahi ango” Ta fada babu ko kishi sai ma murmushi da yake fuskarta. Ta kalli yaranta. “Ku tafi falo, Abba zai zo ya hada muku breakfast yanzu” “Okay” Suka tashi suka fice daga dakin har karamar dake jikinsa. Kamar ficewarsu kawai yake jira sai ta kwantar da kanta a kafadar Hafiz tana kallona. “Amarya karki ji haushi, dan Allah ki yi hakuri, jiya na kasa rike zuciyata ne shiyasa na yi kuka a gabanki ashe kuma wani abu zai biyo baya, bayan haka ban ma san na yi ba sai kusan azuba nan na samu kaina, uanzu haka jiri nake ji ina son na shiga bandaki na kasa” “Ba komai Allah ya baki lafiya” Na fada ina kallonta cike da tausayawa, shi kuma ya kai hannunsa ya daga ta daga kafadarsa yana tambayarta. “Baki yi Sallah ba?” “Na yi sallah ina son shiga bandaki ne na yi fitsari amman na kasa sai jiri nake ji” “Lemme help you” Ya fara kokarin kamata sai ta mike tsaye tana narke masa a jiki kamar wadda bata iya tafiya, ni kam sai mamaki yadda yake da kokari nake ba ma jin tsoron kar aljannunta su tashi ta makureshi. Bandakin suka shiga ya rufe, ina zaune shiru ina kallon furnitures din na ji an bude kofar kadan ta yadda za a iya jin sautin saukar ruwa ko murya. Kamar yadda na ji karar ruwan can kuma sautin karar kiss ya fara tashi. I was like da gaske kissing juna suke a bandakin? Mamaki da kunya suka baibaiye ni. Can kuma na ji ta ce. “Dan Allah ka daina kai da kake da Amarya” Kamar dai ta fada ne domin na ji, saboda muryarta yana daf da kofar bandakin. Ban ji me ya fada mata ba domin bana jin tashin nasa sautin, sai na ji ta kyalkyale da dariya sosai. “Lafiya ta samu kenan tun da kika yi wannan dariyar” Wannan karon na ji furucinsa domin yana daf da kofar ne a yayinta ita kuma ta bude kofar ta fito. Muna hada ido sai ta yi murmushi ya rika ta zauna bakin gadonta. “Angon Noor ya kamata ka shiryawa amaryar abun karyawa, ni ya kamata na yi amman jikin ba dadi” “Karki damu, yanzu zamu dafa wani abun” Ta leko ni. “Kanwata kuma yar'uwarta me kike son ki ci?” Shi ma ya juyo yana kallona da alama amsata suke jira. “Duk abun da ya samu, ba ni da zabi” “Da dai kin fada zai fi, kar mu ba ki abun da ba shi kike ci a gidanku ba, ya bata miki ciki” Furucinta na karshe sai na ji kamar bakar magana ta jefa min, kamar dai tana nufin babu a gidanmu na zo inda ke akwai. Hafiz na ji yace. “Indan wannan ai ba matsala Noor tana son dadi sai idan bata samu ba, haka ne Amarya” Na yi kamar ban ji shi ba, ban kuma amsa masa ba har ya mike tsaye ya karaso inda nake. “Madam a ba ni aron amaryar nan ta rika min wani abu a kitchen na rage mata kadaici” “Aa ban yarda ba, ba zaka gajiyar min da kanwa ba, kana ganinta ka san yar hutu ce bata saba wahala ba, ba yar kananan mutane ba ce ai, ka tafi kai da yaranka ku yi aikin” “Amarya karki zancenta tashi mu tafi” Na mike tsaye a zatona da gaske yake, sai na ji tana masa gargadi cikin wasa. “Barrister, ka san doka ka san Shari'a ka bar min amaryata mu yi hira” Ya juya yana kallonta da dariya. “Au amaryarki ce ma?” “Eh mana abun ka ai abuna ne, ko kana da ja? Yanzu na zubar maka da hakware” Ya girgiza kai ya daga hannu sama like yayi surrender sannan ya fice daga dakin. Na yi murmushin zamantakewarsu ta burge ni sosai, yadda bata nuna min kishi bata nuna masa sai na ke jin kamar ta cancanci a bata kambun Sarauta na Matan Arewa. “Amarya zauna mana, amman fa karki yarda ki ba da ni, ba'a yi ma Namiji rawar jiki, Na ga yana cewa ki tashi muje kika tashi, ai mace yar sarauta ce da isa, balle kuma ke da ba wani son shi kike ba, Wallahi ki rika ja masa aji, gaisuwa ma idan ba shi ya fara yi miki ba karki yarda ki fara gaishe shi, kullum shi yake fara gaishe ni da safe ya bincika lafiyata idan na tashi kalau, and most of aikin gidan yawancin shi yake yi ban cika yin aiki ba gaskiya, Barrister yana da kirki ba ko wace mace ke samun irinsa ba” Na sauke kaina kasa ina tunawa da gaisuwar da yayi min da dazun. Ta gyara zama tana fuskata. “Akwai abubuwa da ya kamata ki sani a tare da mijinki, sannu sannu zan fada miki In Shaa Allah, amman dai ina shawartarki ki rage rawar jiki, ba ayi ma namiji haka kara ki rika nuna masa alfarma kika masa fa kika aureshi damam can ba son shi kike ba kuma ya sani, kin gan ni auren soyayya muka yi ni da shi, amman ya sha wahala kamin na amince masa a shimfida, haka ni ma na sha wahala suma na biyu, ban taba jin azaba irin ta ranar ba, Barrister ba shi da tausayi a wannan bangaren” “Suma kuma?” Mamakin suma ya mantar da ni mamakin fada min sirrin aurenta da nake ganin be kamata ta yi ba. “Kwarai kuwa? Kawayena ba su fada miki ba? Wata kila saboda sun san baki son auren ne, ba dan kar na daga miki hankali ba da sai na turo miki wasu littaffan kin karanta ki fahimci yadda abun yake domin na fahimci ke yarinya ce kurciya na damunki” Gaba daya ta firgita min kwakwalwata, daman ni ina jin cewar ba zan iya yarda wani namijin da ba Zafeer ba ya aikata wani abun da ni balle kuma yanzu da ta fada min waye Hafiz ko kuma na ce Barrister kuma ai ba zata masa karya ba a matsayinsa na matarsa uwar yaransa kuma mace mai kirki. “Amman...” Ta yi hanzari yi min alama da na yi shiru tana nuna min kofar dakin da Barrister ya turo ya shigo, yana Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un. “Me ya faru?” Ta tambaya ni da ita muka kallonsa cikin tashi hankali. “Momy ta kwanta dama, mahaifiyar Kareem ta rasu yanzu...” “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Ta fada ni kuma na mike tsaye da sauri ina kuka. “Wayyo Allah Kareem, ya rasa uwa na shiga uku... Allah kadai ya san halin da zai shiga, dama matarsa da bata da kirki, amman uwa akwai ciwo yanzu zai shiga damuwa sosai, wayyo Allah Kareem...” Kuka nake sosai ina fadin haka, na dafe zuciyata ina girgiza kai, har cikin kahon zuciyata nake jin tsananin tausayin Kareem ya kamani. Daga Hafiz din har matarsa tsayawa suka yi kallona. _______________________ Toh fa Anya akwai Uwargida mai karfin zuciya da iya danne kishi ta rike kishiya a matsayin yar'uwa kamar yadda Matar Hafiz ta yi? 🤔 Ko wane hali Kareem yake a yanzu 😪 Ya zamanta kewar Noor zata kasance a gidan Hafiz? Ga tafiyar dai mun fara... 😊 #KhadeejaCandy as always... 👌 #TKZMAPAID PAGE 2️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ “Daman kin san ta ne?” Na juya na kalleta sai na girgiza kai har lokacin ina kuka sosai. “Aa ni ban ma taba ganinta ba, Kareem ne ya ba ni tausayi, zai shiga damuwa sosai yanzu” “Daman duk mai rai mamaci ne, Addu'a kawai suke bukata, amman wannan kuka haka ai ko mahaifiyarki kika rasa iyaka kenan” Ban sake ce mata komai ba, wata kila ita din bata shaku da iyaye ba shiyasa bata san zafin rabuwa da su ba. Barrister kuma ya sauke ajiyar zuciya ya kalleta. “Ki yi hakuri Noor kowa baya wuce lokacin, bari na tafi gurinsa yanzu” Ya juya ya fita daga dakin, ni ma na bi bayansa, yana shiga dakina ya dauki makullinsa ya fice daga gidan. Ni kuma na kife kan gado ina wani irin kuka sosai mai ban tausayi, Kareem kawai nake hangowa irin halin da zai shiga, ni kaina da na yi rashin uwa a kusa da ni ya kasani wani kalar hali na kunci da kewarta balle kuma ace ta tafi kenan har abada, ga shi ba dadin matarsa yake ji ba, Allah kadai ya san halin da zai shiga a yanzu. Ban wuce minti talatin da shiga dakin ba, macen dake fadar jiri na daukarta bata iya bandaki sai gashi ta kawo kanta a bangare kamar ba ita ba. “Amarya har yanzu kukan ne? Ayi hakuri mana duk mai rai a mamaci ne” Ta zauna kusa da ni tana fadar haka har da kai hannu ta shafa bayana alamar rarrashi. “Hmmm ina mamakinki a haka ma kina tausayin Kareem, ina ga ace kin san abun da aka boye miki?” Na tashi zaune ido da hawaye na kalleta. “Kamar ya? Bata mutu ba kenan ko kuma me?” “Aa ta rasu fa, ba akanta nake magana ba akam Kareem din kansa” “Me kike nufi?” “Sannu a hankali zaki san abubuwa da yawa kanwata, matukar idan muka yi sirri zamu haka rame mu bunne babu wanda ya ji, yanzu ma din ma zuwa na yi na roki wata alfarma a gurinki” Na goge hancina ina kallonta. “Ta me?” “Dan Allah ko da yan'uwanki ko yan'uwan Barrister sun shigo karki fadawa kowa cewar ba ni da lafiya, irin wannan rashin lafiyar ta aljannu ba abar yayata ba ce, kuma ba kowa zai fahimta ba, duk abun da aka yi a gidan nan ko tsakanina da ke ko da mijinmu karki bari kowa ya ji, ko a musulumcin ana son rike sirri, shi ne yarda kuma namiji yana son mace mai tsanannin rikon sirri, tsakaninki da shi dabam, haka kuma sirrin dake tsakanina da ke dabam” Na daga mata kai cike da gamsuwa. “In Shaa Allah Madam ba zan fadawa kowa sirrina dake ba, kuma ba zan fadawa kowa baki da lafiya ba” Ta yi murmushi “Madan kuma?” “Haka na ji Barrister yana fada, ban san sunanki ba” “Sunana Aisha, sunan Madam suna ne da Barrister ya saba min da shi, ni kuma nake masa lakani da Barrister, amman ke zaki iya kiransa da sunansa kai tsaye daman ba son shi kike ba balle na ce ki yi masa sunan soyayya, ni kuma ki kira ni da Sunana Aisha bana son wani Anty ko Yaya ko Maman wani balle Madam” Me yasa Hafiz ya fada mata bana sonsa? Gashi sai yawan nanatawa take ina jin wani iri, ko da yake gaskiya ta fada bana son sa dole ce aka yi da kuma kaddarowar Ubangiji. “Tohm In Shaa Allah” “Yauwa, bari na shiga ciki na yi wanka na ji jikina ya dan saki” “OK” Ta tashi ta fice daga dakin, ni kuma na shiga bandaki na wanke fuskata ina jin cikina na kukan yuwan. Misalin Goma mutane suka fara shigowa yan ganin amarya daga yan'uwansa daga bisani kuma nawa yan'uwa suka fara zuwa. Babu wanda na jidadin zuwansa irin Hana domin jiya ba da ita aka zo ba, a yau kuma ita kadai ce zan iya fadawa damuwa. Domin na kasa sakewa kowa ya kalli fuskata ya san na sha kuka sosai idona ya nuna haka. Wata kila wasu daga yan'uwa mahaifina da suka san bana maraba da auren za su yi zaton wannan kukan na kiyayyar auren ne na yi, yan'uwan Barrister ma sai na ga jikinsu yayi sanyi sosai sai kallona suke kasa kasa ba su wani dade ba suka tafi bayan Zainab da Yar Fulani da Hana sun girka abincin rana. Haka Aisha ta shigo aka yi ta hira da ita sai kusan karfe hudu sannan Hafiz ya dawo gidan ba tare da ya shigo bangarena ba ya dauketa suka tafi gidan mutuwar. Sai da mutane suka fara ragewa sannan Hana ta saka ni a daki muka zauna ta ce. “Noor ina dalilinka na kuka uwar abokin mijinki ya mutu? Uwar mijinki ce balle hakan ya dame ki? Ina ruwanki?” “Hana akwai tausayi fa, Wallahi Kareem yana da kirki kawai dai raba ni da Zafeer da zama sila ne nake jin na tsane shi, kuma ki duba yadda muka ji da Mama ta tafi balle kuma ace uwarta ta mutu fa” “Akwai tausayi amman be kamata ki rika kuka haka ba, ke dai kina kukan auren ne ko? In ba haka ba ban ga ta inda mutuwar uwar wani ta shafe ki ba, Noor ki natsu dan Allah kin ga auren nan an riga an daura ki yi hakuri ki zauna ki bar wa marar da kunya, gashi kin samu kishiya ta kwai inda har ba munafurci take ba to tana da halin kirki, yanzu idan wani abu ya faru kin san Baba ke zai dorawa laifi, kuma Mama zata shiga tashin hankali, gidanki yayi kyau sosai, kowa sai magana yake, kuma mutumen yayi miki hallacci sosai be kamata ki bijiro masa da wani abun na rashin dadi ba, ki duba yadda kika bar gidanmu yanzu ke mai yanci ce sai abun da kike so kike dafawa, ko ki ci haba Noor dan Allah ki natsu” A nan kuma sai na ji kewar rayuwar gidanmu ta dawo min sabuwa, sai na ji babu dadi. Ban raina kaina ba sai da za su tafi da magariba, bayan sun gyara min gidan ko'ina fess, suka jera min lefen da suka zo da shi a cikin Wardrobe dina. Har gurin Gate na rakasu na tsaya daga jikin gate din ina kallonsu har na daina hangosu sannan na juyo na dawo cikin gidan kamar wata marainiya, ina ta jin kadaici da kewar gidanmu, gashi an kawo ni a gurin wanda bana so kamar yadda matarsa Aisha take ta yawan fada. Duk yadda ake yawa kyaun falon da dakina ni dai na runtse ido ban ga kyau a makamata ba. Wata kila saboda hankali be kwanta da auren ba ne ko kuma dai saboda kyalkyali duniya baya gabana a yanzu. Na ji kewa na ji kadaici da tsoro kamin Hafiz ya shigo bangarena domin na ji tsayawar motarsa tun bayan da aka gama sallah Isha'i sai dai be samu shigowa bangarena ba sai tara da yan mintuna. Wike na yi masa da ido ina kallonsa kamar mai jiran ya fada min wani abu, sai yayi murmushi ya tsakali hancina da keys din motar dake hannunsa. “Wannan idon da aka sakar min fa? Babu sannu da zuwa babu komai” Na sauke idon kasa ina jin haushi yadda ya taba min hanci. “Amaryata, kin yi sallah” Na daga mishi kai ba tare da na kalleshi ba, sai ya cire hular kansa ya aje ya fara kokarin cire tufafinsa, ina ganin haka na tashi na koma falo na zauna na bar masa dakin. Sai kusan goma ya fito daga dakin sanye da wata sabuwar Shadda, yana ta kamshin turare ya zauna kusa da ni. “Me kika ci?” Ya taba bakina sai na kauce. “Na ci abun da aka dafa kadan” “Ta so mu tafi Wani guri mai kyau mu siye wani abun sai mu dawo, ban samu riko komai ba saboda mun dawo gida jikin Madam sai a hankali yayi zafi sosai, amman dai na kira kanwarta zata so ta taya ta kwana” “Ni ba sai na je ba, zaka iya tafiya ka siyo ai” “Idan haka kike so, ba matsala” Ya kai bakinsa zai sumbanci bakina na kauce da sauri na tashi tsaye na bar gurin na koma dayar kujera na zauna. Murmushi na ji yayi mai sauti ya girgiza kai sannan ya mike tsaye. “Hafiz” Na kira sunanshi sai ya juyo ya kalleni. “Amaryata ba ki ji sunan ya miki girma ba? hafiz kai tsaye” “Toh ai sunanka ne?” “Haka ne to amman yanzu ni ai mijinki ne” “To ya zan ce maka? Mijina?” Yayi murmushi. “Fada min abun da kike son na siya miki?” Na sauke idona kasa ina taba hannuna. “Daman ina son na tambaya Ya Kareem yake?” “Da sauki?” “Yayi kuka?” “Wanda ya rasa uwa ai dole yayi kuka Noor, uwa ba wasa ba” A take idona ya cika da kwalla. “Yayi kuka sosai?” “Namiji ne shi ai, a boye zai yi” Na dada noce kaina kasa domin bana son ya ga alamar hawaye a idanuwan nawa. Bw sake ce min komai ba ya shiga dakina be jima ba ya fito ya fice. Misalin Sha daya ya rabi ya shigo bangaren nawa a lokacin ina kwance kan gadona na yi shiruuu ni bana tunani kuma bana kuka, babu damuwa babu kuma farinciki a tare da ni. Not too good not too bad. Ina kallonsa har ya sauke ledadin dake hannunsa sannan ya karaso inda nake kwance ya shafa bayana, hakan ya saka ni hanzarin tashi zaune na buge hannunsa. “Ka daina taba ni bana so Hafiz” “Hmmm zaki saba” Ya fada yana murmushi, ni kuwa gabana sai faduwa yake ina yawan tuna labarin da Aisha ta fada min akansa. A daren mun samu aiwatar da sallah nafila da ba mu samu damar gabatarwa ba a daren da ya gabata wadda shi ne darenmu na farko. Ya cilasta min cin naman kazar da gas meat da ya siyo daga wani restaurant din, duk yadda nake da kwadayi da son dadi sai na kasa sake jiki na ci komai gaba daya komai ya fice min a kai. A gurin kwanciya ne aka fara samuwar drama domin ni ba zan yarda na kwanta gado daya da shi ba, musamman da na lura da yadda yake ta son taba a lokacin da muke cin abinci, baya ko taya abokinsa jimami kirkiri zai taba yar mutune saboda babu kunya a idonsa. “To yanzu ya kike so ayi?” Ya tambaye ni yana sanye da kayan bachi kalar nawa da ya saka min a lefe. “Ka kwanta a kasa ko kuma ni na kwanta a kasan kai ka hau gadon” “Ba wani abu zan miki ba Noor, ba zan miki komai ba” Na ga gaskiyar hakan a muryarsa da fuskarta amman tsoro da yawan tunawa da maganar Aisha ya hana ni yarda da shi. “Zan kwanta a karshen gado kai ka kwanta a farko?” Sai na ga kamar ransa be yi dadi ba, sai dai hakan be hana shi amincewa ba kuma be hana shi karfafa min guiwa da murmushi ba. Yadda na fada haka aka aiwatar ni na kwanta a karshen gadon shi kuma a farko da na ji ya motsa sai na tashi zaune, gashi na hana a kashe wutar dakin. Shi kuma ya tsare ni da ido sai kallona yake ya ki ya juya ya ki yayi bachi, ni kuma da zarar na fara bachin sai na kokarin kwatar kaina kar yayi min nauyi mu hade a guri daya. Dariya na ji yayi yana shafa kansa “Kina wahalar da kanki Noor, shureshure be hana mutuwa, kuma ni idan na ce zan yi ko ba zan yi ba, ta zauna domin magana daya nake yi, so ki matso nan ki kwanta kina bukatar hug ki yi bachi mai dadi” Na yi kamar ban ji ba, na ki na motsa ma balle har ya ga dama ta, a haka dai har bachi barawo ya sace ni, wannan karon ban sake farkawa ba sai da ni da shi muka ji karar bugun kofar falo da karfi. “Subhanallahi Lafiya?” Ya fada yana tashi zaune, ni ma na tashi zaune cike da tsoro jikina har rawa yake domin na ji bugun kofar ne a cikin bachi hakan kuma ya tsorata ni sosai. “Bari na duba” Na sauko da kafafuwansa a kasa ya nufi kofar dakin ya bude ya fice, tsoro be bar ni na tsaya jiran tsammani ba na bi bayansa na tsaya daga jikin kujerar falon dake nesa da kofar falon. Wata matashiyar yarinya ce da ba zata wuce shekaruna ba ta shigo falon da sauri tana kuka. “Wallahi Yaya ba zan iya da Anty Aisha ba, ihu take tana makure kanta ta ki ta yi bachi, haka ta shiga dakin su Ikram tana ta dukansu cikin daren kuma ba su mata komai ba, sai zaro ido take” hafiz ya juyo ya kalleni sai ya miko min hannunsa. “Zo mu je?” Na lake kafada a bata fuska alamar ba zan je ba, ahh daman idan ba cuta ba ta ina zai ce na zo muje kuma ya ji kanwarta na fadar tana makure kanta har ta doki yaranta. “Okay Na'ima shiga ku kwanta tare, bari na je na dubata” Yarinyar da ya kira da Na'ima ta nufo ni shi kuma ya fadada kofar ya fice. “Sannu an tashe ku kuna bachi ko?” “Ba komai ai, zo mu kwanta a nan shi sai ya kwana tare da ita a can” “Tohm” Ta shigo har cikin dakina. Ni da ita muka kwanta a kan gadon, a nan kam na samu natsuwa ni da ita muka yi bachinmu cikin aminci da kwanciyar da hankali. KAREEM POV. Sai da ya runtse ido ya girgiza kai sannan ya dan samu saukin jirin da yake gani, sai ciwon kai kam kamar an kara masa wani haka yake ji, ba wani uban nauyin da zuciyarsa ta yi. Cike da karfin hali ya taka ya karasa gurin da Yusura take zaune ya cire drip din dake lake ya saka mata wani sannan ya koma ya zauna ya dafe kansa. Can kuma ya dago kai ya kalli matarsa da har yanzu bata san inda hankalinta yake ba tun bayan da uwar da take kallo a matsayin tata ta kwanta dama, wata kila kaddarar ta mata nauyin dauka ne shiyasa kwakwalwarta ta rikice, domin mutuwa gaskiya ce mai tsananin daci, kuma nauyi ne da idan ya hau kai ba a iya saukewa. Ta rasa mutane masu muhimmanci a rayuwarta tun kamin girmanta ta saba da rashi, sai dai mutuwar Momy ya zo mana a wani ma'auni mai tsanananin nauyi da ya wuce sikelin awa, a yanzu jin take bata da kowa kuma bata da gata domin ta rasa macen da ita ce komai nata kuma ita ce gatanta. Kallonta yake irin kallon da be taba samun damar yi mata ba, tun bayan da ya aureta, ashe ta zama babbar mace wasu abubuwa sun sauya daga hallitarta, sai dai kyaun da Allah yayi mata yana nan har yanzu ko da yake kyauta baya gabanshi sai dai ba zai iya karya ba matarsa tana da kyau. Dauke kansa yayi idonsa na tara kwalla tunawa da ranar da Momy ta fada masa ra'ayinta na son ya auri yar'uwarsa. Wannan karon ba bakinciki auren yake ba bakincikin rasa first love dinsa yake, be saka mata ran mutuwa nan kusa ba, yanzu da waye zai zauna yayi hira irin wadda ya saba yi da ita, wa zai tsokana wasa da wa zai yi shawara...? Shi kam dai be san zafin rashin rai ba, sai a wannan karon ganin yake kamar wata karya ce dake kokarin zame masa gaskiya tsakanin jiya zuwa yau saboda rashin saka mahaifiyarsa a ido da be yi ba. Wai Momynsa ta tafi kenan tafiyar da babu dawowa? “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Ya furta a hankali yana saka hannunsa ya dafe kansa. Hajiya Hassana ce ta shigo dakin dauke kofin fura. “Kareem karbi ka sha, tun jiya na lura baka ci komai ba, tun shekaranjiya ba idonka har ya fada” Ba dabi'arsa ba ce yi ma na gaba da shi musu dan haka na karba ya sha rabi kofin ya aje yana amsa mata. “Eh ni ma na yi wannan tunanin idan har bata samu sauki ba yau dole na kaita asibiti” “Dole kam, Allah dai ya sauwake mutuwa ai ba ku kadai kuka ji ba, ni ma na rasa abokiyar zama mai kirki mai hali na gari” Hajiya Hassana na fadar haka ta fashe da kuka, daman tun rasuwar Momy take ta kuka har ta bawa mutane tausayi. Kareem ya mike tsaye ya fice daga dakin, harabar gidan ya fita gurin da maza suke zama ya zauna kusa da Hafiz yana amsa gaisuwar da ake masa. Kadan daga cikin dabi'u na mutuwa shi ne bata manta gidan kowa, kuma idan ta ziyarta, sai ta bar tabon da ba zai goge ba kuma ba za'a manta da ita ba, mussaman washe garin sadakar uku a ranar kuka yake sosai, daga ranar kewa zata fara domin mutanen dake bada hakuri idan ana kuka sun watse mutum kadai za a bari da kuncinsa a zuciya. Ranar da Momy ta cika kwana hudu da rasuwa, Yusura ta samu karfi jiki a yayinda Kareem kuma ya rasa nasa saboda garkuwar jikinsa dake yin kasa tana son kwantar da shi. Har suka dawo gida wasu ba su daina kira suna masa gaisuwa ba, wasu kuma da kansu suke zuwa su yi masa gaisuwar da ba su samu zuwa yi ba a lokacin da ake zaman makokin. Yau ma kamar shekaranjiya da jiya yana sauke wayar a kunnensa ya mike tsaye ya nufi hanyar kitchen coffee ya hada ma kansa ya fito nufi sama, yana hawa ya shiga dakinsa kansa na tsananin ciwo, zaunawa yayi bakin gadon ya sha coffee kadan ya aje ragowar ya kwanta ko zai samu ciwon kan yayi masa sauki. Few minutes bachi mai nauyi yayi gaba da shi, bachi irin mai tsanannin nauyin nan da ka dade baka samu yi ba, domin har Yusura ta turo kofar dakin ta shigo be ji ba tana fadin. “Makota mu sun shigo, mijinsu yana son yi maka gaisuwa” Jin shiru ya saka ta shiga cikin dakin abun da bata saba ba idan yana cikin, kamar mai shirin yin sata haka ta karasa gurin gadonsa ta so take ta gani bachi yake ko kuma dai ya shareta ne ya ki ya amsa mata. Sai ta same shi a takure ya rumgume hannayensa a kirji kamar wani karamin yaro marar gata sai numfashi yake da karfi. Dillll sakon kar ta kwana ya shigo wayarsa karkata kanta ta yi ta kalli gurin da wayarsa take aje kusa da kofin Coffee. Ta saman screen din wayar ta fara hango sunan Safeena hakan kuma yana nufin sakon ya fito ne daga gurinta... Sosai ta kura ido tana son me sakon ya kunsa sai dao babu dama domin rubutun be fito sama ba sai suna kawai... Dauke kai ta yi ta juya ta fice daga dakin a hankali. Daman har yanzu Kareem yana da number wayar Safeena a wayarsa? Ta tambayi kanta sai dai abun da ta manta zuciyarta bata da amsar tambayarta..... #KhadeejaCandyPAID PAGE 3️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ “Wallahi Bachi yake kusan tun da aka yi rasuwar nan baya samun bachi, yanzu yanzu ya shiga amman har bachin ya dauke shi” Ta fada bayan ta zauna, cike da tausayawa Neighbor din ta ce. “Ayyah ai kara da kika bar shi ya samu bachinsa kam, an kwana biyu ba a runtsa ba saboda damuwa, idan dai ya tashi ki fada masa mun zo yana bachi muna masa gaisuwa” “Okay an gode ki fadawa Baban Ammar din Bachi yake” “Zan fada masa, Allah ya jikanta da rahama kun yi rashi babba” “Sosai haka Allah ya so, sai hakuri” Yusura ta mike tsaye ta rakata har kofar falon da gaisa da mijinta sannan ta dawo falon tana tafiya kamar zata fadi, domin ita ma lafiyar bata wadace ba, mutuwar Momy ta taba ta sosai. Gurin da ta tashi dazun ta sake zaunawa idanuwanta suka cigaba da hasko mata hoton suna Safeena da ta yi arba da shi a wayar Kareem, wani abun da bata saba ji ko sha'awar aikatawa sai shi ne sanin dalilin Kareem na aje number Safeena har yanzu. Cike da son sani me sakon ya kunsa ta juya kanta sama ta kalli upstairs. Tsohuwar budurwarsa ce zai iya ajewa saboda tunawa da ita, waya sani ko suna gaisawa ma. Wata zuciyar ta fada mata. Amman fa tana da aure ko dai auren nata ya mutu ne? Saboda me zai aje Number matar aure a wayarsa, ita ai tana yin aure ta goge number tsohon saurayinta ta toshe duk wata hanya da zai iya jinta ko ta ganshi. Ko da yake ita ai mace ce shi kuma Kareem namiji ne, akwai banbanci koma dai miye su suka sani hakan be dame ta ba. Ta daga kafadunta sannan ta mike tsaye ta kashe wutar falon ta haura sama zuwa dakinta. KAREEM POV. Ya farka a makare gajiya da kuma bukatar da bachin yake da shi a jikinsa, ya hana shi sanin safiya ta waye har sai da rana ta fito misalin Bakwai da rabi. Shi da Yusura ba su saba tashin juna da asuba ba, balle ta shigo ta tashe she ko ta duba lafiyarsa, kara shi wani lokacin ya kan duba lafiyarta idan ya san ta kwanta da ciwo ko kuma aka wuni be ga alamar motsinta ba, domin ya san hakki nw da ya rataya a wuyansa kula da lafiyarta cinta shanta tufatarwa da kuma kwanciya. Ya farka cike da nauyin jiki da kuma zafin zuciya as well as na idanuwa, because he had a dream last night Momy zata tafi Ummara ta bar shi yana ta kuka yana hugging dinta yana rokon kar ta tafi ta bar shi. And when he wake-up he realized ta tafi kenan tafiyar da babu dawowa no more Momy Alive. Sai dai a mafarki ko a tunani ko hoto, he lost her forever. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un...” Ya fada cike da bakinciki biyu, bakincikin rashin Momy da kuma na rasa sallah asuba da yayi gashi yau friday. Wani dogon numfashi yaja ya sauke sannan ya runtse ido ya girgiza kansa dake ciwo. It take him 20 seconds kamin ya sauko ya shiga bandaki yayi wanka yayi alwala ya fito ya gabatar da sallah. The second thing da yayi shi ne daukar qur'ane ya karanta. Yayi ta karatun har tara na safe sannan yayi addu'a yayi ma mahaifiyarsa, a nan ya ji ya samu relief na kuncin dake zuciyarsa even though ba zai tana fita kunci rashin uwa ba har abada. Gefen gadon ya nufa ya zauna, ya dauki wayarsa miss calls din Daddy ya fara cin karo da shi sannan na Safeena ga kuma sakonta na jiya da dare da kuma na yau da safe kamar yadda ta saba aiko masa na safe dare rana amman be tana bata amsa ba, kuma be taba amsa kiran da take masa ba, tun Momy na ciwon har ta rasu. “Kareem ka ki ka kula ni, damuwarka ta haifa min da damuwa, na san rasa uwa akwai ciwo shiyasa nake kira na sanyaya maka zuciya” This is the first time da ya ji he don't need her in his life irin totally, domin mahaifiyarsa ta shiga tsakaninsa da ita lokacin da take raye, yanzu ta tafi ba zai iya cigaba da kula ta ba, and maganar da suka yi na karshe ya gama fahimtar rayuwarta da kuma waccece ita. Goge sakon yayi sannan ya kira mahaifinsa suka gaisa. “Yaya kake Kareem?” “Ina lafiya Baba” “Alhamdullahi, Allah ya kara sanyaya maka zuciya, i know it hurts alot amman ka yi hakuri haka rayuwa ta gada, kuma mu ma can zamu tafi sooner or later...” “Haka ne Baba Allah kasa mu yi kyakkyawan karshe” “Ameen Allah ya maka albarka” “Ameen thank you” Ya sauke wayar ya mike tsaye sai ga kiran Safeena ya shigo wayarsa. Saka wayar yayi aljihu ba tare da ya amsa ba ya dauki abubuwan bukata ya nufi madubi ya fesa turare ya fice daga dakin. Yana karewa falon kallo ya sauko kasa wutar falon a kashe dinning babu abinci, kitchen din ya leka sai ya samu wutar a kashe komai a watse da alamar yau bata shiga sauko ba. Kofa ya nufa har ya murda ya bude sai kuma ya rufe ya sake komawa sama wannan karon dakin Yusura ya tura ya shiga sai ya samu wutar dakin a kunne amman bata cikin dakin. Bathroom ya nufa ya bude ya leka sai ya hango ta zaune a kasa hawaye na mata zuba idonta sun kumbura. “Baki da lafiya ne?” Ta ki ta kalleshi. “Lafiya kalau” “Ina Tine?” “Sun tafi school, na ba su kudi su siya wani abu school” “Kukan na minene?” Na yi shiru. “Magana nake miki fa” “Ba komai” Ta amsa tana matse kwalla, a tsawon rayuwarta bata san samu ba sai dai rashi, ta rasa uba tun tana ciki, ta rasa uwa bayan ta zo duniya ta rasa wanda take tsakanin kauna a matsayin miji, yanzu kuma rasa Momy macen da ita kadaice gatanta a duniyar nan, duk wani shiri da kudiri da take da shi da take jiran mutuwar Momy. Shiga yayi bandakin ya kamata ya mikar da ita tsaye ya fito da ita ya zaunar da ita kan gadonta, a kan madubin dakinta ya aje keys da mini boxes din dake hannunsa ya fita, kasa ya sauka ya hada mata tea domin ya san ita bata shan coffee, ya hado mata da ruwa ya sake haurowa ya shiga dakin ya aje mata tare da cup. “Ki sha zaki samu sauki” Ta kalleshi tana jin wani irin tsanarsa a zuciyarta fiye da kullum. “Me yasa muka yi ma Momy karya? Me yasa muka rayu akan karya? Yau ina bakinciki ina jin ciwon yadda na boyewa Momy irin zamantakewar auren da muke yi” Kareem ya dauki keys dinsa. “Ko ba komai ta tafi tana farinciki da aurenmu, ta tafi cikin kwanciyar hankali da jin cewar ta yi abun da ya dace” Ya juyo ya kalleta. “Ko yanzu lokaci be kure ba Yusura, zaki iya samun farinciki zaki iya auren wanda kike so ko da kuwa kin haifi yara dari, ki daina jin cewar Momy ta tafi ta barki tare da ni zaki dauwwama a bakinciki na har abada, Ba ni da matsala Yusura ko kadan, ki dan ba ni lokaci Bana son mutane su fara tunanin na fara cutar da ke bayan rasuwar Momy, be kamata aji cewar wani abun ya taso a tsakaninmu ba a yanzu” Ta kai hannu ta share hawayenta wasu na zuba. “Kullum cutar da ni kake Kareem, mafi munin abun da a yanzu na gano, shi ne rayuwar auren da muke yi a karya, rayuwa da kai a karkashin gida daya, yana tauye ni, ganinka a kullum yana kara min bakinciki, Yanzu taya zamu fuskanci duniya mu fadawa kowa gaskiyar da muke boyewa? Waye zai fahimta? Wane za a dauka gaskiyarmu ko karya?” “Zan sama miki yanci Yusura, zan wanke ki a idon duniya, za a jinjina miki a san kin yi ma Momy kawaici, Kareem ba zai sake zame miki matsala ba na miki alkwari...!!!” Yana kaiwa nan ya dauki boxes din ya fice daga dakin ta bishi da kallo tana jin wani sabon kuka yana baibaiyeta. Ta sani Kareem yakai ko wace mace ta yi fatan kasancewar da shi a miji, idan har za a so shi dan kyau ko kudi ko asali ko mutunci, sai dai ita bata duba wannan a so, bata taba jin kaunarsa ba, kuma bata taba fatan kasancewa da shi ba har abada. Saboda tana jin shi ne silar rabuwarta wanda take tsananin kauna ido rufe, domin shi ya fara amsawa Momy cewar yana sonta alhalin ya san a kasan zuciyarsa baya son ta, ita kuma da aka waiwaya ta gefenta sai ta kasa musawa saboda gudun kar duniya ta zage ta, Momy kuma ta ga kamar ta yi mata butulci. Idan har so gaskiya ne! Haka ma kiyayyah gaskiya ce! Kareem ya kai namiji amman bata sha'awarsa a matsayin miji ko nan da can, ko da ba zata sake auren kowa a duniya ba tana fatan Kareem ya rabu da ita, tana bukatar ta yi rayuwarta ita kadai ba tare da Kareem ba. KAREEM POV. A lokacin da ya isa gurin aikinsa just few people ya duba ya shiga office dinsa ya zauna, gaba daya ya rasa me ke masa dadi a rayuwar duniya, abubuwa sun tsarke masa, idan ya rabu da Yusura ko nan da shekara ne mutane za su ce saboda Momy bata raye ne, sai dai rabuwa da ita shi ne mafi a'ala domin sama mata yancin da take ta dakon zuwansa, sai dai yaransa fa? Ya makomarsu? Me zai fada musu ya makomarsu, and ta ya zai fahimtar da mahaifinsa da Hajiya Hassana Step mother dinsa da sauran yan'uwa na kusa cewar yana son rabuwa da Yusura ko nan gaba ne? Tunani be bar shi ya ji yunwar safe da rana ba har sai da ya bar asibitin ya isa restaurant dinsa domin baya sha'awar komawa gidansa a yanzu. Yana faka motarsa harabar kiran Safeena ya shigo wayarsa rejecting yayi ya saka ta a blacklist for the second time, sannan ya fito motar yana kallon motar Hafiz dake fake, rufe motar yayi ya nufi reception din. A office dinsa ya samu Barrister yana waya da wani akan wani case da ya shige musu duhu, ya zauna fuska ba yabo ba fallasa ya aje keys dinsa ya kwanta jikin kujerar kana kallonsa zaka san akwai damuwa a tattare da shi. Barrister ya sauke wayar yana kallon abokinsa cike da kulawa. “Doctor dan Allah ka sassautawa zuciyarka, na san akwai matukar zafi da radadi na rasa mahaifiya, amman na daure kai namiji ne, namiji kuma ya saba daukar abubuwa irin wannan, Momy yanzu addu'a take bukata” “In Shaa Allah, ina ta kokarin danne zuciyata Barrister, ni kadai nake iya jin halin da zuciyata take ciki, amman da sannu komai zai wuce” “Da yardar Allah komai zai zama tarihi” Cewar Barrister yana duba wayarsa dake ringing wannan karon Aisha ce take kiran. Ya amsa ya kara a kunne “Hello Madam...” “Ba Aisha bace Noor ce, Hafiz ina son na tafi gida” “Gida gurin me?” “Ni dai kawai ina son na tafi ina marmarin gidan ne” “Toh yaushe aka yi auren da za ace kin fara fita Noor?” His last sentence make Kareem ya kalleshi da sauri. “Ni dai ina son na tafi, ai ana tafiya ganin gida ko?” “Eh amman ba yanzu, kuma idan kina son magana da ni irin wannan ki jira mana na dawo sai mu yi magana, amman ba wai ki ari waya ki kira kai tsaye kamar ke kika aje ba ni na aje ba ki fada min zaki tafi gida” Ya yanke kiran rai a bace sannan ya mike tsaye, ba tare da yace da Kareem komai ba ya fice, Kareem din ma binsa yayi da kallo har ya fice. NOOR POV. “Ya kashe wayar” Na fada ina mika mata wayarsa sai na ji babu dadi kamar ya wulakanta ni a gaban matarsa, domin ita shekaranjiya a gaban idona ta kira shi tace masa tana son ta tafi gida kuma ya bar ta amman ni ya hana ni har da kashe min waya. “Wata kila be son ki tafi yanzu ne, kin san baki wani jima da zuwa gidan ba, girma ma yau kika fara, ki hakura sai nan gaba” Na daga mata kai cikin rashin jindadi. “Ai indai Barrister ne haka yake wani lokaci, shi fa abu kadan ya fusata shi, yanzu zai iya zuwa ya rufe ki da fada ma ko kuma ni da na ara miki wayar, kuma baya son yana fada ka yi shiru sai dai ka yi ta amsa shi in ba haka ba, abu kadan ne zai kai miki hannu” Na kalleta da sauri. “Duka kenan?” “Hmmm, bana son fadar wani abun kar ki yi zaton ina tsorata ki ne, amman fa yana da kirki yana aje komai a wadace gwargwadon hali” Na yi shiru ina jin kara tsanarsa a raina daman ba son shi nake ba, balle kuma yanzu da nake ta kara jin halayyarsa. “Me kike girka yau?” “Taliya” Na fada domin ita na fi kwarewa a girkin, ita ma kuma idan ta yi yawa tsabe min take. Ta wara ido. “Eyyy bari na je na dandana na ji” Kamin na ce komai ta mike tsaye ta nufi kitchen nawa da bayan gama girki ban gyara ba na zo na yi wanka na zauna a falon ina hutawa. Bata jimaba ta fito tana fadin. “Amman Noor kamar kin cika gishiri ko?” “Aa daidai na saka sai dai ko idan bakinki ne” “To kam bakina ne, kin san mai ciki komai nata dabam yake, kuma na manta ban fada miki ba mijinki yana son miyar yauki sosai kamar kuka ko kubewa ko karkashi komai dai mai yauki yana son shi sosai” “Okay” Ta fada gabana na faduwa domin ni ba iyar miyar kuka na yi ba, ita ma ta take na yayan talaka balle kuma wani miyar karkashi ko kubewa. “Bari na tafi bangarena na barki ki huta” Da ido na bita har ta fice sannan na juyo ina kallon tv dake kunne. Gaba daya baya jin sakewa a gidan, ko dan ban saba da Hafiz din ba ne kuma matarsa Aisha ko kuma dai dan bana son auren ne oho, ni nake kamar a gidan yari nake rayuwa ba gidan aure ba. Bata wani jima da fita ba na ji tsayawar motarsa wannan karon be shiga bangarenta ba kamar yadda ya saba sai ya shigo bangarena kai tsaye. Juyawa na yi ina kallon kofar Falon da ya turo ya shigo, zan iya fadar cewar be shigo da far'a domin na ga alamar hakan a fuskarsa kuma gashi be yi sallama ba kamar yadda ya saba yi. Sai kawai ya tsaya yana kallona ni ma kallonsa nake ido cikin ido gabana na faduwa domin matarsa ta fada min zai iya rufe ni da fada ko duka. “Wai ke wace irin yarinya ce Noor? Idan na shigo baki san ki ce min sannu da zuwa ba, idan zan fita babu Allah ya tsare ko a dawo lafiya, idan safiya ta waye baki san ki gaishe ni ba, ba dama kuma dare yayi na kai hannu na taba ki ki fara min ihu kamar kanki aka fara hada shimfida, yanzu kuma ki kira ni kai tsaye ki fada min wai kina son ki tafi gida, haka kika ga ana yi a gidanku? Ki gaba daya baki da tunani baki da hankali ba a koya miki zaman aure ba?” Kamar an hura min wuta haka na ji ruwan zafin zuciyata na tafasa. Na mike tsaye cikin fushi na ce. “Ka san yadda nake ai kamin ka auro ni, taya zaka ce ba ni da hankali bani da tunani kuma haka na ga ana zaman aure, kana nufin ba ni da tarbiya kenan? Kuma Aisha a gaba shekaranjiya ta buga maka waya ta tambaya ta tafi unguwa kace mata eh, sai ni da ka raina zaka rufe da fada” “Ke daya kike da Aisha? Shekararta nawa a gidan nan haihuwarta nawa? Ke kuma yaushe kika zo? Noor ko kiran sunana da kika kai tsaye ba tarbiya ba ce, Aisha ma da kanta ta fada min bata jindadin yadda kike fadar sunanta, ko ba komai ta girme ki ya kamata ki ce mata Yaya ko maman wane” “Ba ni da tarbiya Hafiz, ai kasan wacece ni ka san gidanmu miyasa ka yarda ka auro ni? Ko an maka dole ne? Ka raba ni da wanda yake so na ka kawo ni cikin gidanka kuma kana son ka kuntata min, zafin rabuwa da masoyina zan ji ko bakinciki zama da kai” Tsayawa yayi kallona irin kallon nan na mamaki. “Baki da tarbiya Noor, ba a fada miki muhimmancin aure da zama da miji ba, shiyasa kike kallona kai tsaye ki fada min maganar da duk ta zo bakinki, to ni ba irin Kareem ba ne, iskancin da matarsa take masa kwatarsa ba zan dauka ba, ba zan taimake ki na tsamoki daga wannan gidan da unguwar ta ku ba ki zo nan ki hana ni kwanciyar hankali, shiyasa ana kusan auren nan sai da na ce a fasa kika ce a a mahaifinki zai iya fushi da ke, saboda Mahaifinki.... ” Sai kuma yayi shiru, idona cike da kwalla na ce. “Ka karasa mana ka ce mahaifina mai kwadayi ne, saboda ya siyar da mutuncinsa ya siyar da nawa, kana da hujja na siye shi da kudi, amman ni har abada ba zaka taba iya siye ba Hafiz ba zan taba sonka ba” Na wuce shi na shige dakina ina kuka, na bakinciki da Baba ya janyo min daman na san Hafiz ba zai taba ganin kimata ba, duk mace da ta samu uba irin nawa bata dace ba. Na bata minti talati akan gadona ina kuka sannan ya shigo dakin rike da plate din taliyar da na dafa yana nuna min. “Wane irin abinci ne haka? Gishiri yayi yawa kamar zaki yanka halshen mutane? Kuma kin bar kitchen kacha kacha ke baki san ki gyara guri ba? Idan baki canja rayuwa ba Noor Wallahi zaman gidan nan sai ya miki wahala, tashi ki tafi ki girka min wani abincin” Na tashi zaune ina kuka. “Ni ban iya kalar girkin da kake so” Kamar abun arziki sai na ga ya aje plate din hannunsa ya zauna kusa da ni yana sauke ajiyar zuciya ya fara rarrashina. “Shikenan ya isa, yi hakuri na taba amarya hmmm a yafe min kin ji yar Amaryata” Ya kwantar da ni jikinsa sannan ya ce min na tashi mu yi wanka, na san manufar hakan domin ya gwada min ba sau daya ba. Na yi saurin naje jikina daga na shi na tashi daga jikinsa na matsa. Sai ya tashi ya dauki plate din ya fice daga dakin. Ya dade kamin ya sake shigowa ina kallon yadda ya sakawa kofar dakin key hankalina ya tashi na mike tsaye kan gadon ina kallonsa... #KhadeejaCandyPAID PAGE 4️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Zaunawa yayi bakin gadon yana kallona. “Noor dan Allah ki kwantar da hankalinki, abun nan be kai yadda kike tunani ba, kuma ke ba fa jaririya ba ce da za ace idan zan matsa kusa da ki ri rika ihu kina daga hankalinki kamar yar shekara shida, haba Noor tun yaushe muke abu daya gashi har yau nake shirin barin dakinki? Hmmm i promise you i won't hurt you” Ya miko hannunsa gaba daya sai na ji hankalina ya kara tashi, ko da ace ina son shi yadda Aisha ta fada min halinshi yake da yadda zafin abun yake dole na tsorata balle kuma bana son shi. “Zo mana Noor...” Na matsa can nesa ganin ya mike tsaye, ina ganin ya doso inda nake ya rikona na fara masa ihu iyakar karfina irin da na tsira yi masa a duk lokacin da ya nuna zai yi forcing kansa a gareni, sai dai a duk lokacin da na fara ihun yana saurin saki na ya kyale ni ba kamar wannan karon ba, da ya rike sai ya rikide min kamar ba shi ba ya sakar min karfinsa na kasa motsa hannuna ma ihun kawai nake iya yi, kamin mu ji ana dukan kofa da karfi kamar za a ballata, can kuma aka dawo gurin windows din ana bugawa da karfi. Sakina yayi dan dole ba dan ya samu abun da yake so ba, ya sauka daga kan gadon ya dauki rigarsa ya saka ya bude kofar dakin ya fita, ni kuma na tashi zaune na gyara rigata na ina jan numfashi da karfi. Aisha ce ta shigo dakin da gudunta “Noor Lafiya?” Na rumgume jikina ina hawaye sai ta juya ta kalleshi. “Barristers miye haka? Da yamma haka? Wane irin rashin hakuri ne? Sati daya da aka yi a bangarenta be wadatar da kai ba sai ka nuna mata fin karfi da ido na ganin ido? Kowa ya san halin da kuke ciki? Mai gadi ne fa ya fada min ihun da yake ji a nan yayi yawa naje na duba? Yanzu wannan ba abun kunya ba ne? Kuma duk zaman da ka yi be wadatar ba sai ka shiga hakkina? Yau fa zaka bar nan, daga yin auren kuma sai ka fara abu kamar karamin yaro ko wanda ya fita hayyacinsa? Me kake haka Barristers kanka farau auren budurwa?” Ta fashe da kuka ta fice daga dakin, sai ya juyo ya watso min wani mugun kallo. “Kin ga abun da kika ja ko?” Na sauke kaina kasa. “Ke wai wace irin yarinya ce? Wawuya kawai sakarya, marar hankali marar tarbiya” Uffan ban ce masa ba, ba dan kuma bana jin zafin kalaman nasa ba, sai dan na san nice marar gaskiya a nan, be kamata na yi ihu ba amman kuma kiyayyarsa da tsoron da matarsa ta ba ni ba zai bari na zame masa yadda yake so ba. A fusace ya fice daga dakin, ni kuma na kwanta a gurin ban tashi ba sai da aka yi kiran sallah Magariba bayan na yi sallah na fito daga dakin na sai na samu plate din abincin da ya zuba a dazun aje a gurin, kadan na ci na ji gishiri kamar zai yanka halshena da sauri na zubar kasa na kasa hadewa na nufi kitchen da sauri ina taba kofar na ji ta a rufe da makulli a dole na dawo dakina na shiga bandaki na wanke bakina ina mamakin yadda gishiri yayi yawa haka domin na dandana abinci a lokacin da na gama girkin ban ji gishiri haka ba. Dawowa na yi na zauna a dakina domin zuciyata bata raya min cewar Aisha zata iya kara min gishiri a abinci ba balle na zarge ta, da ma dai ace bama zaman lafiya ne, wata kila kuma jika yayi a yanzu shiyasa yayi yawa. Bayan sallah Isha'i na sake fita na taba kofar kitchen din sai na same ta a rufe da alama da Hafiz ya rufe kitchen yayi tafiyarsa ya bar ni da yunwar cikina. Ni nake kamar zan iya jurewa na dan lokaci ne zai hakura ya dawo min da keys din ko kuma ya shigo ya bude min idan ya gaji. Saboda haka na shiga dakina na kwanta cikin tsoro domin wannan ne karo na biyu da na kwanta ni kadai a bangaren bayan kwanan da na yi na daren farko a gidan. Washe Gari na farka da tunanin yadda za'ayi ni ma kanwata Hana ta zo ta rika taya ni bachi idan baya bangarena saboda na rage kadaici kamar yadda ita ma kanwarta Ni'ima take tayata kwana, na yi ta jiran tsammanin ko ko Hafiz zai leko bangare ya duba lafiya kamar yadda yake duba lafiyar Aisha kullum amman shiru ko da yake ni idan yana nawa bangaren yaransa ne suke tashinmu daga bachin safe da muke komawa, yau kuma yana bangaresu wata kila shiyasa be leko nan ba, ko kuma dai fushi yake ne har yanzu be sauko ba? Domin jiyan nan na bata masa rai sosai, to me ya kamata na yi na bashi hakuri? Ko kuma na share shi idan ya gaji ya zo? Ni kadai nake ta sake sake na na rasa makama. Shiru shiru be shigo ba matarsa ma bata leko ni har azahar gashi yunwa sai cini take daman na kwana da ita. Sai kusan uku na rana sannan ya fita ina ganin haka na jikina ya mutu kuma na gane kuskuren abun da na aikata. Falon na dawo na zauna ina jin wata azzababiyar yunwa gashi babu kudi hannuna balle na siya wani abu kuma kitchen da rufe balle na saffara wani abu. A wani taimako na Allah sai ga matarsa ta shigo da sauri bangarena da far'ata kamar kullum ni kuma na dube irin duba na yar'uwa. “Kanwata ya kike?” “Lafiya kalau” Ta yi fuskar tausayi. “Wallahi ina can amman zuciyata na tare da ke ina tausayinki sosai, na san kin sha yunwa yau ko?” Na daga mata kai. “Ya ji haushina jiya ko? Ina son na bashi hakuri amman ban san ya zan yi ba, na ga har ya rufe kitchen din ya tafi da key din haka na kwana da yunwa” “Allah sarki, gashi ya rantse kar na baki abincin da na dafa, saboda na fada masa da ke zan dafa” Na ji babu dadi kamar na yi kuka kuma dai na daure kar na zubar da hawaye a gabanta. “Aisha ki ce yayi hakuri” “Zan fada masa amman ke karki yi saurin ba shi hakuri ki zubar da ajinki, yanzu kin san yadda zamu yi ga kudi 5k ki tafi ki siyo abinci a waje ki dawo ki ci” Na zaro ido da sauri gabana na faduwa. “Aa ba zan iya ba, jiya fa a gabanki na ce zan fita kin ga yadda yake fada shi ne sanadin ma duk wannan abun balle kuma ace na fita be sani ba” “To zaunawa zaki yi yunwa ta kashe ki Noor? Ya tafi da keys din kuma ya rantse kar na baki abincinsa kuma ya fita ya fada min sai bayan Isha'i zai dawo saboda gurin Hajiyarsa zai tafi na bashi abinci ya tafi mata da shi” Na kalli kudin sannan na girgiza mata kai. “Ba zan iya ba, be kamata na fita be sani ba balle kuma ace siyen abinci zai yi fada idan ya ji” “Taya zai ji? Ba zan fada masa ba” Na girgiza kai na lake kafada. “Ni dai ba zan je ba” “Shikenan ni daman saboda ina tausayinki ne, bari na aje kudin” “Sai idan ba a bawa mai gadi ya siyo min” “Maigadin kuma? Ai ba zai yiyu ki aike shi ba, ba zai ma tafi ba saboda gadi yake yi kuma zai iya fadawa Barrister” “Ni dai ba zan iya tafiya ba, sai dai ko ke idan zaki siyo min” “Ni kuma? Da ciki dako dako na tafi siyo miki abinci.? Ina laifina na tausaya miki Allah ya baki hakuri” Ta mayarda kudinta ya fice daga falon, ni kuma na koma na kwanta ina jin yunwar na min yawo a cikin, haka na kwana da wahala da kuka da bakinciki wata zuciyar na cewa na tafi na karbi kudin na siyo abinci domin ba ni da wata mafita bayan wannan, wata zuciyar kuma na fada min na tafi kawai na bashi hakuri kuma na fada masa ina jin yunwa ya ba ni key na dafa abinci domin alama ta nuna ba zai shigo bangaren nawa ba ya duba ni tun da gashi har dare yayi be shigo ba kuma ya dawo. Na tashi ina jin jiri na fita daga bangaren nawa ina sanye da atamfa riga da zane na shiga bangaren Aisha na samu yaranta suna ta wasa a falon ita kuma tana bare giďa. Da far'a ta tarbe ni ta dakawa yaranta tsawa wai su gaishe ni haka suka gaishe ni jikinsu na rawa na amsa ina zaunawa, kana ganina ka san yunwa ta ci ni har ta gaji. “Lafiya Amarya?” “Hafiz yana nan?” Yaransa duk suka kalleni jin na fadi sunan mahaifinsu kai tsaye. “Eh yana nan? A kira Miki shi?” “Eh ina son na yi magana da shi” “Toh” Ta aje plate din giďar ta tashi ta shiga dakinta, bata wani jima ba ta fito ta ce min. “Yace ki jira shi zai yi wanka” “Tohm” Na amsa idanuwana kamar za su yi magana tsabar yunwa dake matsa min lamba. Haka suka bar ni a gurin tun ina jiran fitowarsa har na fara bachi.... Ko da na farka babu kowa a falon sai ni kadai, tashi na yi na kamar zan fadi na fice daga falon na dawo bangarena ina kuka. Indai har horo ne Hafiz ne Wallahi na horu daga jiya zuwa yau kawai... **** **** **** Yusura na kokarin aje remote din hannunta akan Center table ta dago tana amsa sallamar da Safeena take yi. “Wa'alaikusalam” “Sannu da gida” “Yauwa sannu dai” Safeena ta maida kofar falon ta rufe ta shigo cikin falon ba tare da an yi mata izini ba ta zauna a kujera. “Kin gane ni kuwa?” Yusura ta yi murmushi yake. “Ta ina fuskarki zata bace min? Safeena Right” Safeena ta yi murmushi. “Haka ne, na ga kamar ba jiya ba ne abun, ya gida ya karin hakuri? Na zo gaisuwar Momy ne” “Gaisuwa...? Ko dai murna?” Cewar Yusura babu alamar wasa a maganarta. “Ah haba Subhanallahi ana murnar mutuwa ne? Hana dai Yusura sai kace wata kafura” “Na ga abubuwa sun yi ta faruwa ba ki taba zuwa ba, kamar haihuwata sau biyu ina haihuwa da Kareem amman baki zo mana barka ba, sai yanzu?” “Ban ji ba ne, amman ita mutuwa kin san ba a sanarwarta ni fa gaisuwa kawai na zo, ba fada ba ina tunanin yanzu duk mun girma mun zama manya har da yara” Yusura ta yi murmushi. “Haka ne, baya gida amman ki jira shi ba jimawa zai shigo sai ku gaisa” Ta mike tsaye ta haye dama Safeena ta bita da harara tana jin wani masifaffin kishi na cinta. Yusura na shiga dakinta ta fara safa da marwa tana cizon bakinta gaba daya ta ma rasa gane hikimar zuwan Safeena gidan, ko bata rantse ba ta san Safeena ta yi farinciki da mutuwar Momy domin tana cikin manyan makiyanta da suka hana Kareem aurenta. Kasa zama ta yi har sai da ta hango tsayawar motar Kareem a gurin da ya saba tsayuwa sannan ta nufi kofar dakin ta fita, ta san be kamata ta nuna kishi ba domin ba son Kareem take ba, but abun da Safeena ta yi a yanzu kamar cin fuska ne da mutuncinta, kuma idan har Momy zata tsani Safeena ita kuwa bata san dalilinta na kaunarta ba, zuwanta kuma ya nuna ta jidadin mutuwar Momy if not ai tana da number wayarsa sai ta kira shi ta yi masa gaisuwa ko kuma ta same shi a wani gurin. KAREEM POV. A lokacin da ya faka motarsa ya lura da wata bakuwar mota fake a kusa da Entrance din shiga falonsu. Be raba dayan biyu ba ko dai yar'uwarsa ko kuma yan'uwan Yusura ta bangaren uba ne suka zo gaisuwa ko ziyara, ba tare da fargabar komai ba ya shiga falon. Yana rufe kofar Falon Yusura na saukowa ta karaso gurinsa ta karbi Keys din hannunsa da ledar hannunsa tana murmushi kamar ba ita ba, sai kuma ta sumbanci bakinsa. “Sannu da zuwa...” Safeena na kallonsu ta ji kamar ta kama da wuta, Kareem kam be lura da Safeena sai kallon matarsa yake yana mamakin inda wannan ya samo asali. “Ga Safeena ta zo gaisuwa” Ya juya ya kalli saitin da Safeena take zaune tana ci da wuta. Ya tako ya karaso gurin da take zaune da mamaki a fuskarsa. “Safeena? Me kika zo yi nan?” “Gaisuwa...” Ta amsa daker numfashinta na gargada. Ya kalli Yusura sannan ya sake kallon Safeena “Ashe Momy lokaci yayi” “Haka Allah ya so” “Allah ya mata rahama, ya bada hakuri zan tafi” Ta dauki jakarta ta mike tsaye ta fara tafiya kamar wadda ta rikice. “Ka rakata mata, amman karka dade ka ji Babyna... Bari na hada maka ruwan wanka” Kareem ya kalleta sai ta sakar masa murmushi tana masa alama da ya amsa da gira. “Okay...” Ya amsa With so many questions da yake bukatar amsarsu. Sannan ya juya ya bi bayan Safeena da ke tsaye jikin kofar tana jin komai. Rufe kofar falon yayi suka sauka kasa. “Wannan ya zama na farko kuma na karshe da zaki sake tako kafarki a gidana, ba zan daukar miki wannan ba” “Me yasa ka yi min karya? Kace kai da Yusura baku zaman lafiya, kalli yadda ta tarbeka a gaban idona? Da far'a da soyayya, shiyasa gaba daya ka canja min, tun kamin Momy ta rasu daker na samu kanka yanzu kuma baka amsa kirana baka mayar min da amsar sakona” “Safeena ina cikin jimami na rashin Momy a yanzu, bana bukatar wata maganar, abu na biyu kuma ki natsu ki fara tunanin yayanki da mijinki ki cire ni a rayuwarki... Na gane baki da hankali shiyasa har kika tunanin kashe aurenki ki bar yaranki ki dawo gareni, yanzu kuma abun ya wuce da har kin kai ki tako kafarki a gida? Ba zan daukar miki wannan ba, ban hada iyalina da kowa ba” “Idan na ce zan aikata wani abu akanka Kareem baka ganewa, baka amsa kirana kana ta kokarin kauce min a lokacin da nake da tsananin bukatar saka ka farinciki, da kana kula ni da ban zo gidan nan ba, na riga na sabu da kai, na cutu da soyayyarka ba zan oya warkewa ba amman a haka a mahaukaciya kake kallona?” “Taya mahaifiyata zata hane ni da abu na aikata? Taya tana raye zata hana ni aurenki yanzu kuma bayan ta mutu kike tunanin zan iya cigaba da wani mu'amala da ke? Safeena wake-up ki cireni a rayuwarki and i mean it....” Ya bar ta tsaye a gurin ya rufe kofar falon ya shige ciki. “Aurenta ya mutu ne?” Ita ce tambayar da Yusura ta fara yi masa a lokacin da ya shigo falon. Be tunanin ta yi labe ta saurari abun da suke tattaunawa sai idan zuwanta a gidan ne ya bata mamaki. “Me ye ma'anar abun da kika yi?” Ta mike tsaye tana kallonsa. “Irin abun da muka saba yi ne, a duk lokacin da baki suka zo, nuna cewar muna cikin soyayya da kaunar juna. Aurenta ya mutu ne ko kuma kashewa zata yi ta aureka saboda macen da ta yi mata karan tsaye ta bar mata duniyar?” “Miye matsalarki da hakan?” “Kana tunanin zan so abun da Momy ta ki? Har abada...! Ka fada mata kar ta sake zuwa gidan nan ba saboda ni ba saboda yaranka” Ta aje masa keys dinsa da ledar dake hannunta a kujera ta nufi stairs, binta yayi da kallo har ta haye sannan ya zauna yana kai hannunsa ya taba hancinsa. “Kai Mata kuna da wuyar sha'ani” Ya sauke ajiyar zuciya ya mike tsaye ya dauki ledarsa da keys din ya haura sama ya shiga dakinsa... #KhadeejaCandyPAID PAGE 5️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Tsananin yunwar da nake ji bata bar ni na yi bachi ba, haka na zauna a falon ina kuka jikina na rawa ga kuma tsoro da ya baibaye ni. Misalin shabiyu na dare na ji an murda kofar dakin an shigo, na zabura na tashi da sauri ina kallon kofar sai na yi arba da Hafiz sanye da kayan bachi fuska ba yabo ba fallasa ya shigo. “Baki yi bachi ba?” Madadin na amsa sai na duka a kasa ina kuka. “Ka yo hakuri dan Allah, na daina ba zan sake ba, karka min horo da yunwa ina wahala sosai kuma ina jin tsoro” Be ce min komai ba ya nufi kitchen din ya bude, ni kuma na zauna a gurin ji nake ko kallonsa ba zan iya sake yi ba idan be min izini ba, domin na lura babu imani a tare da shi. Shayi ya hada min ya kawo min, sannan ya sake komawa ciki ina jin kamshi yana tashi, ni dai ban yi komai ba ina zaune a gurin da ya bar ni har sai da ya gama abun da yake ya fito da plate din indomie ya aje min. “Taso ki ci” Na taso na dawo kusa da shi na zauna na fara cin indomie yana kallona har na gama ya kawo min ruwa na sha. “Na gode” “Zaki iya kwana ke kadai?” Na girgiza kai. “Ina jin tsoro” “Zan kawo Ikram da Yayarta ta kwana tare da ke, amman Noor ki zama mai tsananin biyayya da gudun bacin rai please, ina da tsananin fushi da fada, amman idan ka iya zama da ni, ba wahala mun saba, kamar yadda yayarki take yi yanzu” Na daga mishi kai. Sai ya kai hannunsa ya shafa fuska yana murmushi. “Ki yi hakuri, be kamata na yi haka ba, amman na yi ne saboda ki gane kuskuren abun da kika aikata” Ya sumbanci kumatuna sannan ya mike tsaye. “Muje ki saka kayan bachinki” “Nan zaka kwana?” Na tambaya ina kallonsa. “Aa yau ai ba girkin ba ba ne dakin Yayarki zan kwana sai nan da kwana biyu zan dawo” Gaba ya saka ni na har cikin dakin na dauko kayan bachina yana kallona na canja arzikina daya ina da zanen dake daure tare da tare da shi na samu na yi dabara har na canja na saka riga da wando na bachi. Cak na ji an dauke ni daman ba wani jiki da ni ba kuma ya fi ni girma nesa ba kusa ba, saman gadon ya aje ni kwance ya kwanta da jikinsa ban gama fahimta ba na ji bakinsa cikin nawa. Na daure ne kawai saboda babu yadda zan yi ba dan ina so ba, ya dauki dakiku a haka sannan ya cire bakinsa ya daga ni ya sauka daga kan gadon. “Ko ke fa amman da ba ni da ikon taba ki sai ihu, kamar budurwar kauye” Na yi shiru ina kallonsa zuciyata na bugawa da karfi kamar zata cire, murmushi yayi min ya juya ya fice. Da gudu na tashi na shiga bandaki na fara korawa bakina ruwa na wanke shi tasss sannan na saka mai goge baki da buroshi na fara goge bakin ina jin kyankyami. Kamar daga sama na ga an turo kofar dakin ta jikin madubi nake kallonsa har ya fito murmushi yake kamin ya kai hannunsa ya cire brush din ya debo ruwa ya wanke min bakin sannan ya sake hade bakinsa da nawa wannan karon da ya cire sai da ya cilasta min hade yawun bakina. “Na hade” “Toh muje ki kwata, kar na sake kissing dinki ki wanke baki daga yau” Na kalleshi kamar na ce wani abu sai kuma na kyale na bi umarninsa. Saman gadon na hau na kwanta ya lullube ni sannan ya fita be jima ba Ikram da Walida suka shigo suka hauro gadon suka kwanta tare da ni. Bachin yayi min dadi sosai domin ban kwanta tare da shi ba, babu fargaba ko tsoro a kusa da ni. Washe gari bayan na yi sallah ban koma bachi ba na fita falon na gyara kitchen na gyara falon na wanke na wanke na goge na goge sannan na dawo na zauna. Zamana babu wuya Aisha ta shigo falon kiran yaranta da sai a lokacin suka tashi bachi. “Amarya ya kwanan kadaici?” Na yi murmushi. “Yara na zo kira, ko sun tashi” “Eh sun tashi bari na kira su” Haka ta bini da kallo har na shiga dakina na taso yaran suka fito, ta kama hannunsu suka fice tare. Dakin na gyara sannan na shiga na yi wanka na fito jikina na ciwo domin ban saba aikin wahala haka ba, mai na shafa na dauki riga da skirt material na saka sannan na shiga kitchen din na dafa shayi da gass na soya kwai biyar na soya dankali na fito na zauna. Ina tsaka da ci Hafiz ya shigo falon rike da biredi ya aje min. “Good Morning” Na amsa da murmushi sai ya gutsuri kwain dake gabana ya ci. “Ashe kin iya soya kwai” Na yi murmushi, ya mayar min da murmushin sannan ya tashi ya fice. Ina gama karyawa na hau bachin wahala idona cike da kwalla indai haka auren yake ba shi da dadi ni dai a gurin, ba zan fita ba ga aiki kullum ga wahalar kyautatawa miji ko baka so... Na yi wannan tunanin na yi wacan har bachi yayi gaba da ni ban farka sai azahar shi ma saboda Aisha ta shigo har dakina ne ta tashe ni daga bachin. “Ke bachin rana kin yi sallah ma tashi mu yi hira” Na tashi ina murza ido, bayan na yi sallah na dawo muka zauna da ita falo tana min hira mafi yawan hallayar Hafiz take fada min marar kyau, tana kara tsorata ni akan mijinta, sai dai abun da ya bani mamaki kuma ya daure min kai shi ne yadda take zaune da shi lafiya babu wani tashin hankali sai soyyayah da kaunar juna. Ba ita ta bar bangaren ba sai biyar na yamma a lokacin ne na shiga kitchen na sarrafa shimkafa da miya da naman kaza na ci, na bar ragowar kamar yadda na kasa cinye kwan da na soya a dazun. Da dare Hafiz ya shigo ya duba ni sannan Yaransa suka shigo muka kwana tare, washe gari ma haka ya na gyara komai na yi wanka na girka shimkafa da wuri, kamin na kwanta bachin kanwarta ta shigo kirana wai yau tana son na shigo bangarenta mu yi hira. Kwasar fafauwana na yi na shiga bangarenta tana ta bani labarin irin soyayyar da suka yi, ashe aure ta yi bata dace ba ta fito shi kuma ya ganta ya nuna yana sonta iyayensa suka amince kasancewar ba masu matsala ba ne, shi yayi mata komai kamar yadda yayi min a aurena, a lokacin ne take fada min shi ya saka ta makaranta ta yi karatu har take aiki. “Amman ban taba ganin kin tafi aikin ba?” Ta yi murmushi. “Yanzu kin ga ina da ciki wata 6 kuma gaskiya bana sha'awar aiki, na fi sha'awar zama a gida yanzu na kula da mijina da aurena, daman dai babu abun da na rasa kawai ra'ayi ne, yanzu kuma na gane hakan ina son zama a gidana ko ba komai hankalinsa zai fi kwanciya za mu kula da shi tun da ba ni kadai ba ce a yanzu” “Haka ne, amman aiki yana da sha'awa ina son aiki sosai” “Amman ke baki gama karatu ba aka miki aure ko? Na ga ke din yarinya ce sosai har yanxu baki gama wayo ba” Na sauke kaina kasa. “Haka ma a gidanmu ake cewa wai bana da hankali ba na da wayo, wai kanwata ta fi ni wayo, amman ni bana ganin haka” Ni da ita muka juya muka kalli kofar falon da aka bude Hafiz ne ya shigo ba a irin lokacin da ya saba dawowa ba, har da yar tsabararsa. “Welcome Barrister” “Yan mata na har biyu, me ake tattaunawa?” “Hira ce kawai ta karatu take fada min tana sha'awar aiki, ni kuma yanzu ya gumshe ni har na aje sai nan gaba kuma idan komai ya daidaita” Yayi murmushi ya miko min ledar hannunsa sai na saka hannu biyu na karba, sai dai na lura kamar hakan be mata dadi ba domin a take fuskarta ta canja. “Aiki kike sha'awa Noor, ni yanzu bana sha'awar mace ta yi aiki, ita ma saboda ta dage sai ta yi ne, zan saka ki makaranta ki yi karatu mai zurfi saboda gaba, amman zancen aiki ba yanzu ba” Na wara ido baki sake kai kace son karatun nake. “Da gaske zaka bar ni na yi karatu?” “Me zai hana ni fa dan boko ne, karatu sai kin ture yarinya” Zan yi magana ta cafke ta nuna masa murnarta a fili na jindadin yadda yace zan yi karatu tana ta yabonsa har da masa godiya. “Ke gani ko ai na fada miki ki kwantar da hankalinki Barr be da matsala ko kadan, shi mai son kyautata ma iyalinsa ba” Annashuwa ta suka fuskarsa. “Wato gulmana kika yi ko? Na kama ki” Sai ta yi dariya tana kallonsa. Shi kuma ya kalleni. “Ba zaki bude ledar ki ga miye a ciki ba Noor” Na bude ledar na ciro gasashiyar kaza da kayan ciki mai Onion and vegetable sai kamshi suke. Leda ta uku kuma faranti ne dauke da yar tsutsar nan da na yi sha'awar ci tun ina zuwa restaurants din Kareem. “Waya fada maka ina son wannan?” “Na taba ji gurin Kareem” “Na gode” Ina fada ina kallonsa gaba daya ya gana faranta min zuciya a yau. “Me aka dafa?” “Ghanian jollof na yi” “Ku kunci kenan?” “Har kunci kenan?” Ta amsa. “Eh mun ci” Na mike tsaye rike da leadar. “Zan tafi bangarena na ci wannan sai na sha tare da tea” “Okay Amarya aci dadi lafiya” Ta fada na fice daga bangaren na dawo bangare na, wanke hannuna ne kawai ya same ni dole na wanke hannun na zauna na fara ci ina jin wani shauki saboda mai da take da shi gashi ta yi laka laka kamar kitsen kilishi. Bayan na gama na wanke hannun na yi alwala na yi sallah ina nade carpet ya shigo rike da plate dake dauke da kayan ciki da kazar da ya siyo dazun. “Kin manta wannan Noor ko ba ki ci.” “Na ci wannan abun na koshi” “Ki aje wannan anjima sai ki ci” Na karba na juya zan fice sai na ji ya rikoni yana kokarin rumgume. “Kin yi min kyau yau fiye da kullum, ko dan kin dan sake jiki kin sake fuskar nan ne” Na yi murmushin yake Ina sauraren yadda yake yawo da hancinsa a wuyana. Sallamar Na'ima ce ta katse hanzarinsa a dole ya sake ni da sauri yana amsawa. Ya fice daga dakin da sauri “Wai Anty tana kiranka” “Okay” Na bi bayansa na shiga kitchen na aje naman sannan na fito na dawo falo na zauna ina kallo. Da zai shigo yi min sai da safe ne yake sanar da ni wai an yi gobara a gidan Baba, hankalina ya tashi sosai jin cewar gidan ya kore gaba daya. “Amman ba a rasa kowa ba?” “Da an rasa rai da Baba ya fada min, kin san baya boyo, amman dai gobe zamu je mu duba” “Da dare nan aka yi wutar?” “Da yamma” “Dan Allah ko zaka kira min Baba na ji shi?” Na tambaya tare da fatar zai karba bukata sai dai hakan be samu ba. “Ki yi hakuri gobe zamu je mu duba” “Tohm” Kusan sai da na yi mafarkin wutar saboda na kwanta a abun a zuciyata, washe gari na gyara komai na shirya da wuri ina gama karyawa ya shigo bangarena da shirinsa muka fita, a nan ma na ga rashin jindadin fitar ta mu a tare a fuskar Aisha domin ta kasa saki fuska kamar yadda ta saba sai ce masa take ya dawo ya ci abincin rana. “Wata kila ba zan samu dawowa ba, ita ma ai zata dawo ta yi girki ko?” Ya kalleni ina zaune a gidan gaba. “Eh” Ta yi mana Allah ya tsare na rufe motar yaja muka kama hanya. Ba mu yi nisa da fara tafiyar ba ya kama hannuna ya rike yana murzawa a hankali. “A kwana biyun nan fa ina ta jin sonki yana kama ni, kin san ni ban san dadin auren budurwa ba sai yanzu, Allah yasa na same ki fiye da yadda bake tsammani” Na yi shiru ba dan ba gama fahimtar inda zancensa ya dosa ba. Shi kuma be sake ce min komai ba har muka isa unguwar, ina kallon gidansu Zafeer dai da idona ya cika da kwalla, a nesa da kofar gidanmu ya faka ba tare da ya kashe motar ba ya ce. “Ki fadawa Baba idan zan zo daukarki xan shigo mu gaisa ina masa jaje” Na kalleshi kadan na dauke kai, wata kila ya fara gajiya da halin Baba ne, ko kuma dai yana jin abun da yake nema a yanzu ya samu shiyasa yake son kaucewa daga jikin Baba. Ko da yake Baba din ne iya masa sai Allah ba kowa ne zai jure ba. Bude motar na yi na fita sai da na isa kofar gidanmu sannan yayi reverse ni kuma na shiga cikin gidan namu da ya kone tun daga waje har cikin gidan. Da gudu na karasa gurin Hana dake kwance tsakar gidan da konuwa a fuskarta zuwa cinyar hannunta. “Innalillahi Hana” Ta fara yunkurin tashi zaune. A lokacin da Baba ya fito bandakin da sauri yaka aje butar ya kalleni yayi murmushi. “Aha ahhh wa nakd jin muryarta a gidan kamar Nooriyya yar albarka” Na juya na kalleshi ina hawaye. “Baba ashe gobara aka yi?” “Kin gani dai haka Allah ya kawo mana, wutar da dare, ina mijin naki? Baki ce ya shigo ba? Kika bar shi a waje? Ba kara ya shigo ya ga yadda gidan yayi ba” Ya fara tafiya sai na dakatar da shi. “Baba ya tafi yace yana maka jaje za ku gaisa idan zai zo daukata” “Au be tsaya ba? Tohmmm... Toh toh ba matsala ai duk daya ne, kuna dai zaune lafiya ko?” “lafiya Kalau Baba, Baba me yasa ba a kai Hannatu asibiti ba? Kuna ce fa” Na fada ina kallon maganin gargajiya da aka shafa mata. “Ina kudin yake Noor? Kin san yanzu abun duniya ba zama yake ba, ban da rayuwa ba ni da komai a yanzu, sai kuma wanda ya ga Allah ya ga Annabi ya kyautata mana, kina kallon yadda gida ya zama kamar kango, abun bakin cikin ma sai da na sake masa sabon fenti” Ya fada kamar zai fasa kuka, na daga kai ina kallon bakin wutar da ya rufe ginin ya hana a gani fentin. “Ai na so Hafiz din ya shigo ya ga yadda gidan ya koma” Na kalli Baba bance komai ba. Kamin ya shiga tambayata ya kishiyata ya zaman gidan Baba wata matsala, na amsa masa da komai lafiya. Ina nan wasu makotan suka shigo jaje suna ta maraba da ganina har suna fadin wai na fara natsuwa saboda na kasa hada ido da su. “Aure na natsar da mutun, wai Noor ce a haka, Allah ya bada zaman lafiya” A fuskar Baba nake ganin yadda kalamansu suka masa dadi, bayan sun fita shi ma ya fita a nan na samu damar hira da Hana tana fada min yadda wutar ta fara. “Daga dakin Mama ta fito, kuma bachin ya mana nauyi duk ba mu san ta kama ba sai da hayaki ta cika gidan, Yaya yana dakinsa na zaure Baba kuma a waje ya kwana ni kadai ce a daki” “Ya aka yi ta kai ga jikinki?” “A lokacin da na farka na ga wutar tana ci sosai har kusan kofa ba damar na wuce ta saman kuma ta sauka kan katifa sai ta kama tufafinmu ceiling saman kuma yana ta narkewa yana fado min a jiki kin san na roba ne idan ya digo kamar fatar zata cire nake ji, sai da Alhaji Bashiru ya shigo ya fitar da ni” “Ni ma ban sani ba sai jiya da dare Hafiz yake fada min, amman Hana baki ma Yaya magana ba ya kai asibiti?” “Ba shi da kudi ai kin ga da ya kai ni, Baba kuma ba zai iya kashe kudinsa ba ji yake hasara yayi, ban dan ma gobarar nan ba jibi za a kawo amaryarsa shiyasa kika ji yana fadar yayi fenti” Na gyara zama ina mamaki. “Auren dai yana nan da gaske?” “Noor to me zai hana? Mama ma aure zata yi?” “Ita ma? Yaushe? A ina?” “Garin nan, wani mai rufin asiri ma kuwa motarsa ma abar kallo ce” Dadi na saka ni murmushi. “A ina Mama ta hadu da shi?” “A cikin unguwa ya zo gidan wani abikinsa” “Amman shi ne ba a fada min ba? Bani da labarin kowa babu mai zuwa gurina kun bar ni can ni kadai” “Noor ba a kusa kike ba balle nace zan taka da kafa na tafi, ba ni da kudin abun hawa kuma mijinki ma zai gaji idan aka ce kullum zai na je” “Ba zai gaji ba ita ma kanwarta tana yawan zuwa ai, ko jiya ma taje kuma baya cewa komai” “Sai na samu lafiya zan zo” Da kanwata da kusan zan iya cewa tawainiyata ma muka sha hira muka koshi, ina ta sake saken yadda zan saci kafa na tafi na ga Mama babu hali, domin na san Baba zai yi fada idan ya dawo be tarar da ni ba, dole a wayar Yaya na gaisa da ita har nake tambayarta ance zata yi aure. “Da yardar Allah kuwa Noor, idan lokaci yayi ai dole za a fada muku” “Mama yaushe zaki zo?” “Yaushe aka yi auren ma balle na kwashi kafafuwa na tafi Noor? Ni fa uwace ba zai yiyu na tafi gidanki ba sai da dalili” “Amman Mama kin ji Baba yayi wuta?” “Uhmmm Allah ya kyauta gaba, Noor ki rike aurenki da mutuncinki, idon mutane yana kanki kowa jiran yake wani abu ya faru da ke, kuma kin ga zaman gidanku nan ba shi da dadi, da alama kuma mijinki mai hankali ne da tunani, kishiyarki kuma ki rike ta da mutuncin kuma ki yi taka tsantsan da ita, ki rika kula da rayuwa na san halinki da sakarci, balle kuma an dauke ki an kai ki gurin babbar mace ina yarinya karama, ta fiki wayo ta fiki hankali kuma ta fiki sanin kan mijinku, ki bi a hankali kuma ki rike addu'a kar na ji kar na gaji wani abu ya faru, kuman ko da wasa bana son na ji kin bibiye Zafeer aure ya rabaki da kowa yanzu” “Toh Mama, zan kiyaye, Zafeer ni ba zan taba yin magana da shi ba, ai Baba yace be yafe min ba idan na yi masa magana” “Toh sai ki kiyaye, ki zauna lafiya a gidanki kin ji?” “Toh Mama” Sallama muka yi sannan ta kashe wayar na mikawa Yaya. “Mahaifiyar Kareem ta rasu ko Yaya?” “Eh kwana uku aka yi ai ba a bude restaurant din ba, sai da aka yi sadakan uku duk mun je masa gaisuwa” “Yayi kuka?” “A gabanmu zai yi kuka? Sai dai a boye ko? Kin masa gaisuwa” “Hafiz be bari na tafi ba matarsa kawai ta tafi, wata kila sai nan gaba idan na fara fita” “Kila” Saman sama muke taba hirar Yaya na fada min Kareem din ya rame sosai abun ya taba shi. Na yi zaton Hafiz zai dawo da rana ya dauke ni saboda yayi min zancen girki amnan shiru be zo ba sai bayan Isha'i a lokacin Baba har ya gaji da jiransa. Yana yin sallama Baba ya tarbeshi jiki na rawa suka gaisa sannan ya shiga nuna masa gidan yana fada masa yadda gobarar ta fara. “In shaa Allah zan kira ka Baba sai mu yi magana na ga abun da ya dace ayi” “Na gode Allah ya saka da alheri ya kara rufa asiri...” Baki har kunne baba yake Fadar haka, sai dai ko kadan ban ga alamar sake fuska a gurin Hafiz ba, yadda yake rawar jiki da Baba ma wannan karon ban ga yayi haka ba. Ba Baba kadai ba ni kadai na yi tsammanin zai bawa Baba kudi ko kuma ya ce akai Hana asibiti amman ba ko daya har muka fito gidan. Na shiga motarsa shi ma ya zagaya ya shiga sai da yayi min wani kallo da ban fahimci ma'anarsa ba sannan ya tashi motar muka fara tafiya. Ban kalleshi ba, sai dai na ji a jikina yana yawan kallon gefe da nake zaune. “Noor na ga kin bata rai, ko kin yi marmarin gida ne?” Na yi shiru bance komai ba, hannu na ga ya mika bayan motar ya dauko kwali ya dora min a cinya. “Ya kamata ke ma ace kina da waya ko?” Na kalli kwalin wayar na kalleshi ina zaro ido. “Tawa ce?” Ya daga min kai, sai na rasa ina zan saka kaina tsabar farinciki domin taba rike wayar kaina ba. Yana faka mota harabar gidan na fita da sauri na shiga bangaren Aisha ina nuna mata wayar, sai ta fini farinciki da jindadi ma ita ta taimaka min na saka sim din ta nuna min yadda ake operating wayarsa. #KhadeejaCandyPAID PAGE 6️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ “Allah ya tsare ya sa albarka” Ta yi min addu'a sai na amsa da amin sannan na karbi wayar bayan ya saka min number shi da number Baba da kuma na Aisha. “Amman fa karki je ki kira Saurayinki da wayar nan na sa halinki” Ta fada tana min wani kallo kamar na zolaya, ni kuwa na kalli Mijina na kalleta da mamaki. “Ya za'ayi na kira sho kuma? Na fa yi aure yanzu na sani” Ta sake fuskar zolaya tana min wani kallo na rashin yarda. “Ke dai kin san yadda muke sirrinmu ko? Kawai dai ki kiyaye, ke matar aure ce a yanzu kin ji kanwata” Na amsa mata da tohm domin kawai na takaita zancen sannan na mike tsaye rike da wayar da kuma jata na fice daga bangaren. Ina shiga bangarena na tare a kujera ina ta kallon wayar bude nan taba nan hotunan da na yi kuma sun fi a shirin a zama daya. Ima tsaya da daukar wani hoton sai hango Hafiz na yi ta cikin hoton ya leko kansa. Na juya na kalleshi ina dariya shi ma dariyar yayi ya matso kusa da ni ya zauna. “Daukin wayar ne har yanzu” “Eh na gode Hafiz” “Ki daina cewa Hafiz Noor” “Tohm Yallabai” A bakin gaskiya ta na fada sai dai na lura kuma hakan dariya ya saka shi domin dariyar yake kamar na fadi wani joke. “Ur Welcome..” Ya kama hannuna na rike ya juyo da kafadata daya na fuskance shi da kyau. “Noor, please karki ba ni kunya i trust you, kar na ji ko na ga abun da zai bata min rai wayar nan, ba ma waya kadai ba a komai ma, kin ga Aisha ta fada min abubuwa da kika fara fada mata akan zamantakewar duka duka kuma yaushe muka fara zaman auren? Sirrin dake tsakanina da ke na mu ne mu kadai kawaye iyeye ko abokiyar zama babu wanda zai sani, wanda ke tsakanina da ita kuma ita ma zata rike babu wanda zai sani, kin ga da farko na ji haushi amman daga baya na yi tunani hankalinki da tunaninki ba irin nata ba shi, saboda shekarun ba daya ba, amman ina son na ja kunnenki karki fadawa kowa sirrinmu kin ji? Kuma zancen baki so na kika aure ni na san wannan ita ma ta san wannan ba sai kin yi ta nanata mata ba kina fada mata yadda na raba ki da saurayinki, yan'uwana ba su san irin auren da muka yi ba, so bana bukatar su san cewar wai baki so na kika aureni kinji” Na daga mishi kai. “Me tace na ce” Na tambaya ina mamaki, domin ban san na taba fada mata wani abu a game da Hafiz ba, yo ni da har yanzu ba mu taba hada shimfida ba ta ina zan fada sirrinsa? Kuma yaushe nake fada mata yadda ya raba ni da Zafeer. “Cewa ta yi kin kura min ido kamar zaki cinye ni” Ya ja hancina hana kallon cikin idona. Na sauke kai kasa. “Baki jin yunwa ne? Ko kin ci abinci a gida?” “Aa ban ci ba, kai baka ci ba?” “Ban ci na so ki dawo ki girka, ni ma ban samu dawowa ba sai daren nan” “Girki cikin dare akwai wahala kamin ka fada na yi bachi” “Wa zai dafa?” Na dan saci kallonsa na sauke ido, ba dai yana nufin ni na girka ba? Ganin na yi ya mike tsaye. “Taso muje mu siyo wani abu a waje” Na mike tsaye ina rike da wayata, a nan na bar jakar da na dawo da ita daga gida. Hannuna ya kama muka fita daga falon be sake ba har gurin motarsa ya bude min na shiga sannan ya zagaya ya shigo ya kunna motar sai kuma ya  kalleni. “Bari na tambaya Madam ko za a siyo mata wani abu” “Tohm” Yana fita na fara daukar kaina hoto a motar, be jima ba ya dawo ya ja motar muka kama hanya. Na yi zaton zamu tafi Kareem Restaurant ne sai na ga ya faka a wani restaurant da ban sani ba, ko'ina na gurin wuta ce mai calar blue da ja daga waje. Ciki kuma farin haske ne irin wanda ko allurarka ta fadi zaka iya gani. Sai da ya fara fita sannan ni ma na fito muka jera a tare muka shiga. “Me kike son ki ci?” “Ice Cream” “Ice Cream ai ba abinci ba ne” “Ni idan na ci shi ya ishe ni, sai kuma nama” Muna tafiya ina fada ina rabon ido, katon guri ne aka yi kowa bangare abu dabam ne, idan zaba sai ka tafi gurin biya ka biya sannan ka fice. Gurin masu pizza ya fara zuwa ya daukar mana daya, ya nufi shawarma ya dauki biyu, sannan muka nufi gurin masu kaza dake cikin gilashin tana juyawa kawar wata karuwa. “Ba mu daya” Ya fada sannan ya kalleni ya ciro wayarsa aljihu da hannu daya ya matsa can gefe yana amsawa. Mutumem ya gama yanka kazar ya saka a leda sai ya miko min, na waiga na kalli saitin da yake tsaye yana wayar da murmushi a fuskarsa da alama da Madam yake waya domin ita ce kadai zata iya saka shi irin wannan murmushi kuma ta dauke masa hankali. Ban bi ta kansa ba na nufi gurin masu ice cream ina duba wanda ya fi girma a jikin hoton dake gaban box din, domin sai ka zaba sannan za a dauko maka. “Wane ya fi dadi?” “Kowane ne yana da dadi yan mata, amman dai ki dauki vanilla ice cream mata sun fi son shi” Na ji an fada daga gefena, na juyo na kalleshi sai ya sakar min murmushi. “Can i pay” Na girgiza masa kai alamar no, sai ya bata fuska kamar mai magana da yarinya. “Why? Baki son na samu lada?” “Kai Malam Lafiya” Hafiz ya fada tun kamin ya karaso ni da shi muka juya kallon Hafiz din da ya daso gurin da saurinsa. “Waye wannan? Yayanki ne?” “Mijina ne” Ya matsa nesa da ni ya kalli daga sama zuwa kasa. “Duk kyaun nan naki, wannan ne mijinki” Ban ce masa komai ba, shi ma kuma be sake cewa komai ba ya nufi gurin biya ya bar shi a gurin tsaye. “Waye wannan?” “Ban san shi ba, yau na fara ganinshi ni ma” “Amman ai magana na ga kina yi da shi” “Tambaya yayi zai iya biya na ce aa ni matar aure ce” Hafiz ya kalli gurin da mutumen nan yake tsaye, shi ma kallonmu yake kamin ya karbi katinsa a fara saka masa kayan a babbar leda. “Mu tafi...” Na wuce gaba yana bayana muna isa gurin Mutumen ya karbi kayansa ya fara tafiya. “Oga Abdull ga canjinka” Daya daga cikin masu karbar kudi a gurin ya fada yana mika masa canjin 750. “Keep the change” Ya fada ba tare da ya juyo ba. Hafiz ya ciri Atm dinsa ya biya kudin aka fara saka mana a babbar leda, a nan na samu damar satar kallon mijin na wa, ni ban taba lura da yanayinsa kyau ko muni ba dress ko yanayinsa, gaba daya babu ko daya a gabana sai yau da mutumen nan yake mamakin ni din matarsa ce. Kuma gaskiya ya fada Hafiz ba shi da wani kyau na azo a gani, ba laifi dress dinsa na zamani riga da wando, kuma yana ta kamshi ba laifi ba zaka kira shi baki ba haka kuma ba fari bane. “Muje” Ya rika duka ledodin gaba ya saka ni sai da na fara fita sannan ya fito. Kamin mu isa motar na hango yarinyar nan da Zafeer yake yi ma gyaran mota tana doso gurin, ita ma kallona take kamar yadda nake kallonsa da alama ita ma dai ta gane ni kamar yadda na wayance ta. “Noor ko?” Ta fada yana nuna ni a lokacin da ta karaso kusa da ni. Na daga mata kai ina murmushi Hafiz ya kalleta. “Wacece wannan?” “Waye wannan Yayanki ne?” Ita da shi kusan a lokaci daya suka yi tambayar kowanensu yana kokarin sanin abun da ke tsakanina da daya. “Mijina ne” Na fara amsa mata jiki a sanyeye ina jin babu dadi domin ta san alakata da Zafeer. A take na ga yanayinta ya sauya kamar mai mamaki kamar kuma bata jidadin amsar tawa ba. “Zafeer...” Sai kuma ta yi shiru... “Allah be yi da shi ba, Noor shiga mota mu tafi” Hafiz ya fada rai a bace yana ba ni umarni. Na nufi motar ina jin wani abu marar dadi ya tokare min zuciya. Kamin na isa gurin motar hawaye ya cika idona har ya fara zubo domin ta tuna da abun da nake kokarin mantawa da shi a kankanen lokaci, mutumen da ba ya kunyar nuna soyayyata a gaban kowa. Tsaye ta yi tana kallonmu har sai da muka bace mata. Kaina a kasa yake har muka isa gida na ki yarda na dago dan kar Hafiz ya ga hawayen dake min zuba, sai dai hakan be hana shi fahimtar kuncin dake zuciyata ba, domin yanayina ya sauka ba kamar yadda muka fita ba. “Mutumen nan kamata yayi ki fada masa kina da miji tun farkon da yayi miki magana, kin san kina burge maza for no reason me ya ba zaki kama kanki ba? Ke komai sai an fada miki sannan zaki yi? Aisha tana da gaskiya be kamata na baki wayar nan a yanzu” Ban ce masa komai fadansa sai kara min zafin hawaye yake. “Ba ni wayar...” Ya miko min hannunsa yana kashe motar. Sai da na hade yawu sannan na mika masa wayar. “Zan baki amman sai nan gaba idan kin yi hankali, yanzu ko na barki da ita hankali ba zai kwanta ba, ai na ga darasi gurin abokina mata ba ku da amana if not taya kina tare da ni zaki zubar da hawaye saboda da wani da ba zai iya zaman aure da ke ba, ba zai iya miki rabin abun da na yi miki ba” Na kalleshi. “Amman zai ba ni farinciki, irin wanda ba zan taba samu a gidanka ba, da baka bar ni tsaye ba ka je kana waya da munafukar matarka ta ya wani zai min magana? Ko kuma an rubuta a goshina na ne cewar ni matar aure ce? Wayarka kuma ka aje bana so ko da nan da tsufa ne, idan ba ka yarda da ni a yanzu ba ba zaka taba yarda da ni ba har abada” Na bude motar na fita a fusace na bar masa kofar a bude ba tare da na rufe ba. Falon na shiga na zauna kan kujera gaba daya na rasa me ke min dadi. A kan kujerar da nake zaune ya watsar siyayyar da muka yi. “Noor For the very last time karki sake kiran Aisha munafuka, ko ba komai ta girme ki, ta cancanci girmama daga gurinki, balle kuma tana matata, ba zan yarda ki shigo gidana ki rainata ba, babu kalar soyayyar da bata nuna miki ba, idan baki gode ba karki zage ta ba zan yarda a raina min uwargidana ba uwar yayana, ki tsaya matsayinki...” Uffan ban ce masa ba na tashi na shiga daki na kwanta kan gadona ina kallon OPO dake dakin hawaye na zubo, haduwata da matar a nan ya tuna min da waye Zafeer a gurina, abu da duk wanda ya san alakarmu zai yi mamakin ace ba shi na aura ba. “Miye wannan?” Ya tambaya a tsawace dagowar da zan yi ya watso min wani abu mai kamar magani a fuska da wata roba. Na tashi zaune na dauki maganin mai kananan yaya na duba, sai wata roba da ban gama sanin ta miye ba guda biyu, roba na fi duba domin ta yi min kama da balloon sai dai ta banbanta da ballon sosai, ba kuma zan iya fadar ko ta miye ba domin ban san amfaninta ba. Na sake duba maganin shi ma wani kalar magani ne mai 2 colors da ban taba ganin irinsa ba. “Miye wannan.?” Ya daka min tsawa har sai da hankalina ya tashi, gaba daya fuskarsa da hallitarsa sun canja jikinsa har rawa yake kamar zai doke ni. “Ban san ko miye ba...” “Karya kike munafuka, a jakarki na ganshi yanzu waya baki ina kika siya?” Na girgiza kai amman na kasa magana domin tsoron fushinsa da nakr gani a yanzu ya cika zuciyata. Furta cewar a jakata ya gani ya saka na sauka da sauri da zimmar na tafi na duba jakar tawa da na bari a falon sai na ji ya fisgoni iyakar karfinsa na wulgar da ni kan gadon. “Ina zaki je? Ba zaki fada min ba? Uban waye ya baki wannan maganin? Ina kika siya? Mi ya kawo condoms a jakarki?” “Wallahi ban sani ba... Ba.. Ba.. Ban saka.. Magani ba... Ni ban...” Na kasa magana tsoro da kuka suka ci karfina, ban san me yake fada ba maganin ne condoms ko kuma robar, ko ma duka? To miye illarsu? Miye kawo su a jakata? Taya? Ya hauro saman gadon da talkaminsa ya riko ni da duka karfinsa. “Ina kika siye Noor? Saboda me kika siya?” “Ban saya ba, ban san amfaninsa ba, ni ban saka komai a jaka na ba, ban san maganin miye ba, ban san robar ta miye ba, ba nawa ba ne Wallahi” “To ina aka samu ya aka yi na ganshi a jakarki?” Na rike hannunsa daya jikina na rawa. “Wallahi Wallahi ba nawa ba ne, ban san miye ba” “Da na aje ki gidanku ina kika je?” “Ban tafi ko'ina ba Wallahi” “Amman kin yi magana da Zafeer?” “Ban yi ba, Wallahi ban ga Zafeer ba” “To wannan abun su suka kawo kansu a jakarki kenan?” “Wallahi ban san na miye ba, Hafiz sai idan saka min shi aka yi a jaka..” Fwauuu ya buge min baki. “Ban ce ki daina fadar sunana ba? Ke gaba daya kanki babu tunani babu tarbiya babu hankali? Gaba daya baki da lissafi? Waya saka miki maganin to? Waye? Ko ki fada min ko na ci ubanki da duka Wallahi” “daga gida ban je ko'ina ba, kanwata kuma ba zata saka min wannan abun ba, ni da ita duk ba mu taba ganin wannan abun ba” “To waya saka miki? Ina kika samu? Ni zan dauko na saka miki a jaka?” “Sai idan Aisha ce ta saka min saboda ta yi min sheri, Wallahi ban san na miye ba” Ina fadar hakan sai ya sake ni, ya sauka daga kan gadon ya fita daga dakin. A nan an samu damar daukar maganin na duba na sake duba balloon din har biyu sannan na nufo falo na duba jakata da ke kasa sarka da yan kunne da na cire na saka a ciki tun a gida suna watse a kasa. Naira biyar ma ba ni da ita a jakar to a ina zan siye magani? Kuma maganin miye zan siya, wane chemist bayan cikin gidan mu ban san na taka ko'ina ba. Ban gama shiga tashin hankali ba har sai da Aisha ta shigo falon tare da Hafiz. “Noor ni na saka miki magani da condom a jaka? Ta ina? Da zaki fita na karbi jakarki ne? Kuma ai tare kuka dawo da Barrister idan na saka miki wani abu a ciki zai gani, Kuma na rantse da Allah bayan fitarku ban shigo dakin nan ba, me zai saka ma na yi haka?” Ta juya gurinsa da sauri ta zube kasa. “Na shiga uku kar ta kashe min aure, daman burin yan matan yanzu kenan, Wallahi ba ni na saka, idan ni na saka mata shi a jakarta kada Allah ya ba ni abun da nake so Wallahi ba ni ba ce Barrister Innalillahi Na shiga uku...” Ya rika ta ya mikar da ita tsaye, gaba daya sai suka daure ni na rasa ya zan zarga ita ko kanwata? Ko kuma shi da ya saka min jakar a lefe? Yanzu ta ya zan wanke kaina. “Tafi bangarenki” Ta kalleni tana kuka. “Allah ya saka min gareki, na barki da Allah saboda kar a zarge ki shi ne zaki maida laifin a kaina? Ba ni ba ke Noor daga yau kowa ya tsaya bangarensa....” Na kasa cewa komai sai kallonta nake hawaye suna sauko min kamar ba gobe. Ta rufe fuska tana kuka sosai ta fice daga falon, kamar fitarta yake jira ya juyo kaina. “Ta rantse ba ita ta saka miki ba, daman makasudin kiran kenan, fada min ina kika samu wannan? Yanxu kika samu ko kin dade?” Na yi shiru kamar wadda kalamai suka karewa. “Ba magana nake miki ba?” Ya sake daka min tsawa. Still ban iya ce masa komai ba, domin babu wasu kalmomi da zan hada na wanke kaina. “Shiyasa auren mace mai mutunci mai tarbiya da natsuwa yana da dadi, ka aureki saboda na rufa miki asiri amman kullum matsala kike ba ni, ni ban taba samun matsala da matata irin wannan!” Yana matsowa ina matsawa baya jira kawai nake ya kai min duka a jiki domin alamar hakannta bayyana a jikinsa da fuskarsa. Kwafa yayi ya nufi ledodin da muka shigo da su ya kwashe gaba daya ya fice daga falon. Ranar kwana ne amman be kwana a dakina ba sai ya kwana a dakin Aisha, ni kuma na kwana a falon cikin kunci da rudani mai tsananin daure kai. A haka muka kwashe sati biyu be shigo bangare na ba, da girkina da ba nawa ba duk baya zuwa gurina, sai dai na hango shi ta window idan zai fita ko ya dawo. A lokacin damuwa ya fara shiga raina, na tabbatar Zafeer ba zai iya min haka ba, gashi Baba ya aurar da ni ga wanda bana so kuma be iya zama da ni ba. Kukan safe dabam na rana dabam da dare ma idan zan kwanta dabam ga abinci amman bana iya sarrafawa na ci saboda damuwa sai ruwan sha yi babu bread domin ya daina kawo min komai, wani lokacin kuma na dafa taliyar yara kadan na ci. Idan na zauna da tunani sai na rasa wa zan kaiwa kukana, Baba zan je na fadawa ko kuma Mama ko kuma dai Kareem zan fadawa shi da yake abokinsa? Ko kuma gidan iyayensa zan bincika na fada musu ko kuma na zauna a haka? Na zuba masa ido? Gashi babu wani dan'uwa da ya sake zuwa gurina na balle na bude masa ciki na fada masa damuwata. Amman har zuwa yaushe zai yi ta fushin da Ni? Zuwa yaushe zai sauko? Agogon dakin na duba karfe biyu da mintuna na rana, tashi na yi na dauki green hijab dina na saka na dauki jakar nan da na yi fitar farko da ita na sake dauka na bude marfin madubina na dauko balloon din nan da maganin na saka a jakata na saka talkamina na fito falon na leka windows din waje ban motarsa ba hakan na tabbatar min da baya cikin gidan kenan. Bude kofar falon na yi na fita sannan na janyo kofar ba gabana na faduwa na sauka entrance din na nufi gate. Kamin na fice har wani gumi ke karyo min domin idan ya tare ni a kofar gate din ko hanya ban san me zan fada masa ba. Mai gadin ne ya bude min na fita dama ko hagu sai na rasa ina zan dosa can wata zuciyar ta raya min dama domin ta nan muka bi lokacin da zamu tafi gida tare da shi. #KhadeejaCandyPAID PAGE 7️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Na yi tafiya mai nisa kamin na samu Napep na tara ya fada masa inda zai kai ni na shiga. Sai da ya fara tafiya sannan na fara sake saken idan na tafi gida me zan fada? Na nuna musu abun da ya gani a jakar tawa ko kuma dai na fada ma Baba cewar ya daina shigowa bangarena? Gidanmu zan tafi ko kuma na su gidan? Idan ma na ce zan tafi gidansu ina zan bi domin ban taba tafiya ba be kai ni kamin auren ba, bayan aure kuma ba mu samu kwanciyar hankalin da zai kai ni gidan ba. Wata zuciyar kuma na raya min na tafi gurin Mama kai tsaye sai dai kuma ita ma zan iya shafa mata laifi. Ya mace bata da gidan da ya fi na mahaifinta saboda haka na fada masa unguwarmu kai tsaye. Har kofar gidanmu ya faka Napep din na fita na shiga gidan da sallama. Yaya na fara cin karo da shi yana wanki sai kuma Hana dake gaban murhu tana girki har yanzu da sauran kuna a jikinta domin na same ta babu riga a jiki. “Yaya dan Allah dari biyar zaka ba ni zan sallami mai napep” “Lafiya?” Ya tambaya yana kallon yanayi na, domin na shigo gidan ne cike da damuwar da ta kasa boyuwa a fuskata. Na yo shiru be sake ce min komai ba ya tashi ya shiga dakinsa ya dauko dari biyu da naira dari ya miko min. “Su kenan suka rage min, nawa ya kawo ki?” “Ban yi ciniki da shi ba, bari na tambaya” Na juya na fita, ta inda na yi sa'a ina tambayar mai Napep din nawa ya ce min dari uku sai na mika masa na dawo cikin gidan na nufi kofar dakin Mama na zauna. “Noor kin rame? Ko baki da lafiya?” Hana ta fada satar kallon Yaya na yi dake kallona sannan na ce. “Har yanzu konan be warke ba?” “Eh da saura, kin san wuta bata warkewa da wuri, kowa ma cewa yake na yi sa'a jikina yana da kyau ne” “Ina Baba?” “Dazun ya kawo cefa ne ya fita, anjima na san zai dawo cin abinci ai tun da yace ya gama da wuri” Na sake kallon Yaya sannan na kalli rufin kwanon da aka yi da tsohon kwano a dakunan da suke kone, shi ma kuma daga dakinmu sai na Mama da take ciki na Yaya har lokacin a bude yake. “Ashe an rufe” “Eh Ya Nabil ne suka rufe shi da abokinsa, tsofin kwanon da suka kone ne suka rufe da su” Duk maganar da nake Hana ce take amsa min shi dai be sake cewa komai ba sai dai ya kalleni. Ina zaune a gurin har ya gama wankin ya shiga yayi wanka ya fito Hana ta gama girkin ta zuba mana, na samu cin abincin da yawa kasancewar a tare muka ci da ita kuma muna ci muna hira. Bayan mun gama na yi alwala La'asar na yi sallah na zauna akan tabarma ina jiran shigowa Baba har lokacin na gagara fadawa Hana ko Yaya dalilin zuwan nawa. Yaya Nabil yana yi alwalar La'asar ya fice daga gidan, sai ya rage daga ni sai Hana ita din ma na kasa ce mata komai, gani nake kamar yayi wuri na fara fadar matsala wata kila ba za su yarda da ni ba. Shigowar Baba ta saka hantar cikina kadawa na kasa samun sukunin zama sai motsi na ke irin na marasa gaskiya. “Ahh Yau Norriya ce a gidan na mu? Maraba maraba da zuwa Nooriyya an tuna da gida kuma?” Na yi murmushin karfin hali na yi masa sannu da zuwa ya amsa Hana ta dauko masa kujera ya zauna kusa da ni yana kallona far'a kamar na zo masa da albishir. “Ya gidan lafiya? Ina mijinki yana lafiya ko?” “Lafiya Kalau Baba” “Tun dazun kika zo?” “Eh da rana na zo” “Madallah kin ci abinci?” “Eh na ci Baba” “Haka ake so, Mijin na ki dai yana lafiya ko?” “Eh Baba” Na amsa cikin rashin sakewa, tsoron duka ko zagin da zan sha a gurin Baba ya hana ni fada masa damuwar da na zo da ita, haka na hade hannu ina kallon Baba yana cin abinci yana fada min wai kwanan baya ya kira Hafiz a waya be daga ba. “Ina ta saurarensa yace zai kira ni kuma be kira ni, kuma na kira shi be daga ba” “Wata kila baya kusa da wayar ne” “Ni ma na yi tunanin haka, amman ai ya kamata ya kira idan ya ga kiran nawa, amman dai ba komai ai zai zo daukarki ko?” “Eh zai zo, yace ma na tafi gurin Mama na dawo da wuri kamin ya zo” Na yi karya ina jin kamar a gurin mahaifiyata zan fi samun sakewa na fada mata damuwa fiye da shi, da zai iya rufe ni da fada ko duka. “Ah aha shi ne kuma kika zauna har yanzu? Tashi ki tafi mana ga yamma na yi sai ki dawo da wuri karki tafi ki zauna fa, ki dawo da wuri kar zo be same ki ba” “Tohm Baba, amman ba ni da kudin abun hawa” Ya saka hannu aljihu ya ciro tari bakwai ya ba ni. “Tashi ki tafi, karki jima” Na karba da hannu biyu na dauki jakata na mike tsaye ina kallon kanwata. “Tafiya zaki yi” “Eh ba zaki raka ni ba Hana?” Jin haka ya saka ta shiga daki ta dauko hijab ta dora a saman zanen da take daure da shi, na yi ma Baba sallama da zimmar dawowa idan na tafi na fito Hana ta rako ni muka fito. Ko kadan ban yarda na daga kai na kalli kofar gidansu Zafeer ba, saboda ji nake kamar zan ganshi ne ko ya ganni hakan kuma ba zai mana dadi ba dukanmu. Har bakin Titi Hana ta rakoni na tari Napep ina tsaka da ciniki da shi na ji ta dafa ni. “Noor Wallahi yanayinki kamar akwai matsala!” “Akwai, ki min addu'a kawai Hana Allah ya min mafita” “Ameen, je ki dawo sai mu yi magana” Na daga mata kai na shiga Napep din. Yana tafiya ina hawaye har muka isa gidansu kakaninna. Farincikin ganin mahaifiyata da yan'uwanta da kuma su kansu yan'uwan mahaifiyata da suka yi farinciki ganina ya mantar da ni yar damuwar da na zo dauke da ita. Suka kawo min abinci har kusan hudu kasancewar gidan family house ne mai bangare dabam dabam irin na mutanen da da ake zama tare da jikoki da yaya da yan'uwa. Sai da na kebe da mahaifiyata sannan damuwa ta dawo min a take yanayi na ya canja. “Ba zaki ci abincin ba?” Mama ta tambaya, sai na kalleta ta yi jikinta ta yi haske kamar ba ita ba da alama hankalinta yanxu ya fi kwanciya fiye da lokacin da take gidan baba. “Na ci abinci a gida kamin na zo” “A gidan Baban na ki ko mijin? Ance ubanku ma aure zai yi? Kuma mai kudi wai Mama?” Ta yi dariya. “Eh ke ma ai Hana tace min aure zaki yi Mama” “Eh In shaa Allahu jumma'ar nan ta sama za a daura auren, ina son daman sai an kusa na shirya na tafi na ga dakinki, yan'uwa sai yabawa suke, na san dai baki son auren amman ya miki komai Noor domin ubanki ba zai iya zuba miki wannan kayan ba, duk da dai ban gani ba amman ina jin ana ta yabawa” Na yi shiru na sauke kaina kasa. “ina abokiyar zaman naki kuna lafiya ko?” Na dago na kalleta. “Lafiya Mama sai dai...” Sai kuma na yi shiru, ita ma shirun ta yi tana kallona. “sai dai me? Noor karki fara dan Allah, yaushe aka miki auren balle har ace matsala ta fara shiga, shi zaman aure dan hakuri, kina kallon yadda na sha wahala gidan ubanki balle wannan dake kaunarki kamar ya hade, na san halinki Noor shiyasa tun farko na gargade ki, wauta da sakarci sun miki yawa, abun kadan zaki iya ganinsa ba daidai” “Wata kila kuma ni nake da gaskiya Mama” Na fada murya kamar zan fasa kuka, idona na tara ruwan hawaye. Sai ta hade min rai ta dauke kai. “Bana son na ji, indai shi ya kawo ki gidan nan, to tashi ki tafi ba ki zo ganina cikin dadin rai ba sai zaki kawo min wani korafi? Je ki samu Babanki shi da ya daura miki auren ki fada masa, sai ni da kika raina, salon ace ni yanxu zan yi aure ke kuma na kashe miki aure? Noor kin san iya idon da yake kanki kuwa? Ana kalle da ke ana jiran wani abu ya faru, aure kasa da wata daya ki fara zuwa zaki fada min an miki ba daidai, daman miki daidai sai Allah Noor ki rufa ma kanki asiri ki zauna dakin mijinki, in har kika ce haka zaki fara da shi, to ko ba zaki taba zaman auren ba, ni bana son na ji komai tashi ki koma dakinki” Kamin ta gama bayanin kuka ya gama cin karfi, haka na tashi ina share hawaye na saka hijabina na dauki jakata na fito gidan ana sallah magariba. Hanya na kama na rasa ina zanje, yanzu kuma waye zan fadawa kukana? Ko dai na tafi gidansu? Kuma da wane idon zan kalli iyayensa? Me zan fada musu cewar ya ga wani abu a jakata yayi fushi da ni? Wata kila ya ji haushin haka ko kuma su ma su kasa fahimta kamar yadda shi ma be min uzuri ba, gashi ban san gidan na su ba. Ko dai na koma gida? Kuma idan na koma haka zai cigaba da yi min na san zuwa yanzu kuma ya dawo be same ni a gidan ba. A take zuciya ta raya min na tafi gidan Kareem na fada masa halin da nake ciki na fada masa abun da abokinsa yake min wata kila zan samu mafita, domin ina jin babu dadi yadda ya wofintar da ni babu ruwanshi da ni akan laifin da ban aikata ba. Mai napep din da na shiga be sauke ni ko'ina ba sai kofar gidan Kareem. Na bashi kudin Napep 400 sannan na doshi kofar na buga mai gadin ya bude min. “Dan Allah Kareem yana ciki?” “Gaskiya yana ciki be dawo ba, amman dai iyalinsa tana nan” Sanin halin matarsa na rashin maraba da mutane, da kuma kokarin fasa min kai da ta yi a wacan karon ya saka ban yi sha'awar shiga ciki na zauna a gefen gate din cikin flowers din da suka yi ma gidan ado. Ina zaune a gurin har aka kira sallah Isha'i aka sauko daga sallah sannan motar Kareem ya tsaya a gaban gate din yana horn. Na mike tsaye da sauri na nufi gilashin motar na kwankwasa sai ya sauke farin gilashin yana kallona. “Noor...” “Na'am” Na amsa ina hade hannayena waje daya yanayina na karantar da duk wanda ke kallona damuwata. “Ke da wa kika zo nan? And lafiya?” Hawaye ya fara sauko min. “Kareem ina cikin matsala, kuma ina jin kai kadai zaka iya taimaka min, dan Allah karka ce ba zaka saurereni ba, ina jin tsoron Baba na kasa fada masa kar ya kure ni ko ya min duka, Mama kuma ta ki ta saurare ni” Ya dan tsaya kallona kamin ya ce. “Shiga cikin gida” Na wuce sai da na fara shiga sannan na shigo da motarsa ya faka kusa da ni, ya bude ya fito ya kalleni. “Hafiz ya san kin zo nan?” “Aa be sani ba” “Me ya faru?” Na hade yawu. “Baya shiga bangarena yau kusan sati biyu, baya min magana matarsa ma fushi take da ni, ba ni da walwala Kareem gaba daya na ji na tsani gidan na tsani kaina” Ya ciro wayarsa ya fara tabawa. “Wani abun kika masa ko?” “Ban masa komai ba, kawai dai wani abu ya gani a jakata ya fara fada....” Na fada masa komai cikin kuka. “Minene to?” Na Cire jakar daga kafata na bude na dauko maganin da balloon din na mikawa Kareem.  Sai yaja baya da sauri kamar ya ga abun kyama. “What the F**uk, miye hadin ki da wannan Noor” Na kalli maganin na kalleshi. “Na minene? Ban san maganin miye ba Wallahi, wannan ballom din ma ban taba ganin irinta ba, Wallahi Wallahi ban san ko abun miye ba Kareem” “To ya aka yi kika samu?” “Ban san ya aka yi ba kawai shi ya ganshi a jaka” “Wannan maganin hana daukar ciki ne, wannan kuma Condom ne” “To me zai hada ni da maganin hana daukar ciki? Wallahi ban san shi ba ban taba ganinshi ba ma, ban san inda aka siyarwa ba, shi condom din me ake yi da shi?” Yayi shiru yana kallona. “Bayan aurenki baki hadu da Zafeer ba?” “Aa Wallahi ban sake ganinshi, kuma Baba yace idan na sake magana da shi be yafe min ba, ance ma ya tafi baya garin nan” “Akwai mai shiga dakinki ko ya taba jakarki?” Na girgiza kai alamar aa. “Dole akwai yadda aka yi Noor magani ba zai kawo kanshi ba, dole akwai yadda aka yi” “Ni dai na yi zargin Aisha amman tace ita bata saka ba, ban san ya zan wanke kaina ba Kareem, yanzu baya min magana kuma baya shigowa gurina fushi yake da ni” “Me yasa kika zargeta?” “Saboda tace wai na fada mata sirrinsa kuma ban taba fada mata ba, kuma a gabansa tace na ce zan kira saurayina a waya kuma Wallahi ban taba ce mata ba” “To kin taba barin jakarki a bangarenta?” “Aa, amman Wallahi ban san a ina aka samu maganin ba, ni ban taba ganin wannan ballom din ba ban san me ake yi da shi ba” Yayi shiru alamar tunani ni ma shirun nake ina hawaye. “Kawo?” Ya miko min hannunsa na bashi maganin da  balloon din ya saka aljihu, sannan ya dago ya kalleni ido cikin ido ya sauke ajiyar zuciya. “Noor ba zan iya miki komai ba, sai dai na baki hakuri, akwai dalilin da ya san ba zan shiga maganar ba” “Wallahi ban san wanda ya saka ba Kareem ba nawa ba ne” “Na yarda da ke Wallahi Noor i trust you, ko ma waye yana son yayi amfani da innocent you ya cutar da ke, Hafiz ya san abun da baki sani ba a game da ni, ba zan iya shiga maganar nan ba, wata kila shiga ciki zai iya janyo miki matsalar da ta fi wannan ba, iyaye ya kamata ki samu da wannan maganar iyayenki ko nasa” “Baba ba zai yarda ba, Mama kuma bata ma saurare ni, ban san gidansu ba, kuma idan naje wata kila ba za su yarda ba” Ya busar da iskar bakinsa damuwa ta bayyana a fuskarsa. “Kawai ki yi hakuro Noor ki tafi gida kar ma ki fada masa kin zo nan” “Tohm” Na share hawayena wasu na sauko min na juya na fara tafiya, sai ya kira ni. “Noor” Na juyo. “Kina da kudin Napep?” Na girgiza kai, sai ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudi 2k ya ba ni, na karba ina kallon matarsa take tsaye jikin windows din sama tana kallonmu, shi ma daga kai yayi ya kalleta. Na juya sai kuma na sake juyowa a karo na biyu na kalleshi. “Kareem ya keke?” Yayi min kallon rashin fahimta. “Rasuwar Mahaifiyarka ban samu yi maka gaisuwa ba, amman abun yana raina, na san kai ma kana cikin wata matsala kuma na zo maka da wata am sorry...” Yayi min murmushi kawai. Ban sake cewa komai ba na kama hanya ina tafiya hawaye na sauko min har na fita cikin gidan. Ashe haka auren yake, ashe haka rayuwar auren take? Idan mutum yana cikin matsala babu wanda zai saurare shi, babu mai kawo masa dauki, shiyasa Baba yayi ta ganawa Mahaifiyarmu Azaba kala kala kuma ake ta ba shi gaskiya a duk lokacin da za a fadi matsalar. A lokacin da na tari Napep na hau sai fargaba ta ta koma gurin hukuncin da zarar tarar a gida, domin be min izini ba na fita gashi kuma dare yayi ban dawoda wuri ba, kuma abun da naje nema ban same shi ba. Dubu daya na mikawa mai napep din da ya kawo ni gida, ban tsaya karbar canjin ba na shiga ciki, ina hango motar Hafiz wani irin faduwar gaba da tsoro suka mamayeni, a haka dai na daure na karasa bangare na taba kofar falon na murda sai na ji ta a rufe na sake murdawa na tura na jita a rufe gam da alama an saka mata key an rufe ne. A gurin na sulale kasa na zauna gaba daya na rasa me ke min dadi. Ina zaune a gurin na hango Aisha ta fito da saurinta ta nufo inda nake babu jimawa Barrister ya biyo bayanta, ina ganin haka na mike tsaye ina kallonsa fargaba ta saka ni gaba kamar ance ga mutuwarki nan zuwa. “Ba magana make miki ba?” “Wallahi Barrister ba zan yarda ba, ko dai ka bude mata ta shiga ko kuma na kaita bangarena ta kwana ko kuma ni ma na bar maka gidan, cikin uku dole ayi daya, yanzu duk abun da ya faru mutane ni za su dorawa laifi, ace na hana muku zama lafiya, babu wanda zai iya wanke ni, Wallahi sai na yi ma Walida tsinanen duka a gidan nan, sai da na gargade ta karta fada maka amman saboda kunnen kashe ne da ita sai da ta fada” “Karki kuskura ki taba min yarinya, kuma ki cire bakinki ki cire idonki akan zamantakewarmu, ba ke kike aurenta ba ni nake aurenta” Yana fada ya jefo min keys din, sannan ya nuna mata bangarenta. “Wuce mu je” Ta share hawayenta, ta dora hannunta a cikinta da be gama girma ba. “Dan Allah Noor ki natsu, ko da baka son auren mutum ba haka ake rayuwar aure ba, be kamata ki fita baki fada masa ba, ki sani yanzu baki da ikon kanki ikonki yana gurin mijinkin ne, kuma idan ba ki yi dan Allah ba baki yi dan shi ba ki yi dan ni mana, Wallahi idan wani abu ya faru tsakaninku ni za a zaga, kuma a zarge ni” Cikin kuka take maganar sannan ya juya ta nufi bangarenta. Tsaye yayi yana kallona irin kallon na tsana da jin haushin mutum, sannan ya juya ya shige bangaren nata. Ni kuma na sunkuya jiki babu karfi na dauki keys din na saka na bude kofar na shiga, na rufe na jingina da kofar falon suuuu na tafi kasa na zauna ina kuka... KAREEM POV. Tsaye yayi yana kallonta har ta fice sannan ya juya ya nufi hanyar shiga cikin gidan. Murda kofar ya shiga. “Sannu da zuwa...” Yusura ta fada masa, sai ya kalleta fuska ya yabo ba fallasa ya amsa. “Yauwa” Ta sabuntawa kanta wasu dabi'u da hallaya da bata masa a baya, kamar kaima masa abinci a dakinsa yi masa sannu da zuwa ko a dawo lafiya idan zai fita. Tun a wacan ranar da Safeena ta leko gidan duk wasu hallaya da dabi'u nata sai suka sauya. Ya wuceta zai haura sama sai ta juyo tana kallonsa. “Ina tunanin a matsayina na matarka ina da hakkin tsare mutunci da martaba ta” Ya juyo. “Akwai wani furuci ko wani aiki da nake yi da ke zubar da kimarki?” “Kamar zuwan yan matanka, ya kamata ka san ina da girma a matsayina na matarka” “Noor Matar Hafiz ce, amaryarsa Safeena matar aure ce miye baki sani ba a ciki?” Ta masa wani kallo sannan ta ce. “Ga abinci can a dakinka” Ba tare da ya sake cewa komai ba ya haura saman ya shiga dakinsa. ko'ina kamshin sinasir yake da miyar da ta ji nama da manshanu. Amman ko kadan be kula abincin ba ya cire tufafinsa ya shiga yayi wanka kmar yadda ya saba ya fito ya saka kayan bachi, daman baya dawowa gidan sai ya cika cikinsa. (Idan kika karanta min littafi baki biya ban yafe ba.) A daren ya kwanta da tausayin Noor da kuma tunanin yadda zai bullowa lamarin, ta ko wane bangare idan ya hango sai ya ga kamar shiga maganar zai iya zama matsala. Sai dai ya yarda da wani abu daya, Noor bata aje maganin a jakarta domin idan har ajewa ta yi ba zata bari ya gani ba, wata kila dai tsakanin Aisha da Zafeer akwai mai shirya mata wani abun bata fahimta ba. Washe gari misalin 7am ya bar gidan saboda operation da za su a 8am a asibiti. Be wuce 10 -15 Min da fita ba Yusura ta shigo dakin kamar yadda ta saba ta fara bude kayan abincin da ta kawo ta ga be ci, daman kuma ta san ba zai ci ba domin yar kullum ce be cin abincinta ita ma kuma bata fasa girkawa. Sai da ta fitar da kayan sannan ta dawo dakin ta nufi gurin da yake aje kayan dauda ta bude ta dauko green shaddarsa ta jiya ta zauna gefen gadon tana lalaben aljihun kowane bangaren. Domin zuciyarta bata natsu da abun da ta hango Kareem ya karba a hannun yarinyar da ta taba fasawa goshi ba jiya... #KhadeejaCandyPAID PAGE 8️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Wani irin faduwa gabanta yayi a lokacin da ta yi arba da abun da ke cikin rigar aljihun Kareem. Me hakan yake nufi Kareem yana tare da yarinyar nan kenan? Ba ita kadai ba wata kila har da Safeena, matan aure yake bi kenan? Shiyasa yake takura mata a lokacin da take fita gani yake kamar ita ma gurin wani zata tafi? Anya ma wannan Amaryar Hafiz ce? Idan har gaskiya ne me zai saka yayi tarayya da ita? Ta mike tsaye da sauri ta fice daga dakin rike da maganin da robar ta shiga dakinta sai da ta dauki wayarta sannan ta tuna bata da number matar Hafiz domin ba kowa take hulda da shi ba a cikin matan abokan Kareem, iyakar ta da wasu gaisuwa. Number wayar Samira ta nema ta kirata suka gaisa cikin mutunci sannan ta bukaci Samira ta turo mata da number Aisha matar Hafiz. “Wai daman baki da number ta” “Ban taba karba ba” “Kai kawata baki da kirki, bari na turo miki yanzu” “Yauwa na gode, Ai na san kuma good time da ita ba zaki rasa number ta” “Okay” Ta sauke wayar kamin Samira da ta kasance cousin dinta ta turo mata mumber Aisha har ta matsu. Sakon mumber na shigowa ta bude da sauri ta taba Number ta kira sai daf da zata yanke Aisha ta daga. “Assalamu Alaikum” “Wa'alaikusalam Aisha ya gida?” “Lafiya kalau ya yaran?” “Alhamdullahi kin gane mai magana?” “Na so dai na gane, amman ban gane ba” Yusura ta yi murmushin karfin hali. “Yusura ce Maman Tine” “Kawai ki ce min Mrs Kareem zan fi ganewa, uwargida ran gida” “Oh oh toh ke ma ai uwargidance, ko da yake yanzu nake jin cewar Hafiz ya kara aure” “Wallahi haka ne, kika ji ko dai Kareem ya fada miki, ai ke ma auna arziki kika yi da yanzu ke za a kawowa ita” “Ban gane ba” Yusura ta fada daman abun da take nema kenan. Aisha ta sauke numfashi. “Hmmm ai mijinki ya so aurenta shi yayi sonta sosai, sai dai ban san miya hana shi aurenta ba, kwatsam Hafiz ya zo min da zancen auren, wai zai rufa mata asiri ya aureta saboda wanda zata aura an fasa auren sanadin Kareem shi kuma Kareem din yace ba zai aure ta ba, kin san mazajen na mu da hadin kai ko ma dai miye Allah kadai ya sani” “Amman kika yarda Aisha?” “au hanawa zan yi? Kin ji Yusura da wata magana, namiji da zai yi aure zaka iya hana shi ne? Ai idan namiji zai kara aure baya ji baya gani, shiyasa na nuna masa na fi shi tausayinta, na san waye Hafiz na gama karantar mijina daman kuma idan ka fahimci waye mijinki zaman aure ba zai yi ma mace wahala ba, shiyasa na goya masa baya dari bisa dubu aka yi komai aka gama cikin mutunci lefen ma ni na hadawa kaina na hada mata, yadda na san Hafiz ina daga hankalin na daga na shi zuciya zata iya dibarsa ya sallame ni gidanmu, amman hakan da na yi sai na siye zuciyarsa da ta yan'uwansa gashi muna zaune lafiya ni gani nake kamar ma ya fi so na yanzu sama da lokacin da be auri yarinyar ba, domin na kara value a idonsa” “Toh Allah yasa yar gidan mutunci aka dauko miki kin san yan matan yanzu” “Waya sani ance dai ubanta dai shegen kwadayi ne da shi ko kashe rai zai iya yi akan kudi, ita kuma gaskiya ance bata tsayawa kanta ba, kawai dai maza ne mace daya bata isarsu sun maida karin aure rayuwa, kuma basa tsayawa su duba yar gidan mutunci daukowa kawai suke, saboda tana da kyau” “Oh Allah ya kyauta, matan zamanin nan sai a hankali” “Ameen kedai ina nan ina lallabawa karta kashe min aure, ga yara ga ciki na tafi ina? Samun miji irin Hafiz a wannan mazanin ai sai an tona is rare gaskiya” “Allah ya tsare miki aurenki, ni ai be fada min ba sai yanzu, na ce dole na kira na miki jaje” “Hmmm na gode, zan yi saving number ki ai a rika gaisawa” “Toh sai anjima” Yusura ta kashe wayar gabanta na bugawa da karfi. What her husband got into? Ko shiyasa ta zo nemansa har cikin gidan kamar yadda Safeena ta zo? Me yake kokarin zama ne? Matan aure yake nema? Ta mike tsaye ta fara tafiya tana daga kanta. Amman ita miye nata a ciki idan ma neman matan yake yi? Kabarinsa dabam nata dabam, kuma bata fatan zama da shi har abada. “Saboda yaranki...” Wata zuciyar ta fada mata. domin saboda su ta dawo tana kokarin kyautata masa tun daga lokacin da Safeena ta leko gidan. Ji take indai tana raye ba zata iya bari Kareem ya auri Safeena ba ko da kuwa bata da aure domin Momy bata son Safeena ko kadan, mutuwarta kuma zai iya saka Safeena ta yi tunanin sake kulla alaka da Kareem. Gashi yanzu babu Momy babu mai masa fada idan yayi ba daidai ba. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Gaba daya ta rasa me ke mata dadi, ta rasa ina zata kama abun ya daure mata kai, wai saboda be sonta yake bin mata ko kuma dai wani sabon hali ne ya kirkirarwa kansa? Tunaninta ya kasa tsayawa guri daya. KAREEM POV. @4:11pm suka fito daga massalacin dake cikin restaurant din, Kareem na gyara hannun rigarsa ya ce. “Ni dai da zaka dauki shawarata Barrister karka karbi case din nan, case ne mai matukar hadari kasan yadda yan siyasa suke” “Amman za a samu kudi mai kyau fa Doctor” “Rayuwa ta fi kudi muhimmanci, duk kudin da zaka samu idan ba zaka samu rayuwa ba ba su da amfani” “Kusan kowane aiki akwai risk ciki, kawai dai ka taya ni da addu'a” “Allah ya tsare, amman ni ban yarda ka karba ba gaskiya” Hafiz ya tura kofar office din ya fara shiga yana fadin. “Su suka neme ni fa, kuma saboda cancanta suka neme ni, ba zan oya watsa musu kasa a ido ba, abu na biyu ba a nan za'ayi ba a Kaduna ne” Kareem ya daga kafadunsa. “Indai ka nace sai ka yi ai babu mai hanaka, haka shi ne kawai matsalata da kai” Yayi murmushi yana gyara zamansa a kujerar da ya zauna. Kareem yayi shiru na yan mintuna sannan ya kalli Hafiz cikin karfin hali ya ce. “Hafiz ya iyalinka?” Wani kallo Hafiz yayi masa a cikin kallon da yake masa idan yana tuhumarsa da wani abun. “Lafiya?” “Ka tabbata?” Hafiz ya gyara zamansa. “Akwai abun da kake son mu tattauna?” Kareem yayi murmushi domin shi da abokinsa kowa ya san halin kowa, da zarar dayan ya fuskaci wani canja ko da na magana ne zai fahimci akwai manufar aikata hakan. “Amm... Ban san ya zaka dauki abun ba, na so na bar maganar sai kuma nake ganin kamar zaka kone kanka ka cutar da iyalinka, be kamata na shiga cikin maganar ba amman dole ce ta saka” Hafiz ya mika masa duka hankalinsa yana kallonsa. “Lokuta da yawa idan ka ga In aikata wani abu da be dace ba kana yawan jan hankali kuma ka lurar da ni gurin da illar abun take” “Ka wuce duk wannan Kareem fada min kawai” Kareem ya zauna da kyau. “Hafiz akwai wata matsala tsakaninka da Noor ne?” Hafiz ya kalli wani gafen alamar tunani sannan ya kalli Kareem. “Ta zo nan ne?” A madadin Kareem ya amsa masa sai ya dora da abun da yake jin kamar shi ne matsalar. “Hafiz ka rika bincike kamin ka yi fushi ko yanke hukunci” “Kareem ta fada maka abun da ta yi?” “I don't think Noor zata yi abun da kake tunani, she's very innocent, Hafiz bata ma san amfanin abun da ka gani a jakarta ba bata san me ake yi da shi ba, kuma abun mamaki ne ace ta san wannan a yanda take da kananan shekaru, she's too young for that ita ba karuwa ba ba matar da ta shekara hudu gidan miji ba” Hafiz ya nade hannayensa. “Idan bata sani ba taya suka zo a jakarta? Kasan dai ba za su kawo kansu ba ko? Idan ba ta siya ba maybe wani ya bata wani like Zafeer amman ta ki yarda ta fada wanda ya bata, ko kuma ya fada mata ta siya, ranar da na kaita gidansu ta wuni a ranar da ta dawo ne na karbi wayar da na bata kawai wata zuciyar ta raya min na bude jakarta and i did na ga abun a ciki” “Taya zata amsa laifin da ba nata ba, bata san ya aka yi ya zo jakanta ba” “Kai kuma ka yarda da ita?” Kareem ya kasa cewa komai wannan babin saboda baya son ya janyo mata laifi gurin Hafiz. “Ya kamata dai ka yi bincike, ta rantse bayan aurenta bata hadu da Zafeer ba ko ta yi magana da shi” Hafiz ya kwanta jikin kujerar. “Wa kake zargi? Aisha saboda ta fada maka Aisha, shiyasa na kirata ai lokacin da ta zarge ta kuma ta rantse a gaban Noor ba ta saka ba, sai me?” “Maybe the way you confront her zai iya sakawa ta rantse ko da akan karya ne saboda ta wanke kanta” “Me yasa ka yarda zata aikata amman baka yarda Noor zata aikata ba?” “Saboda Noor bata waye duniya, da zaka ce min ta shiga gidan mutane ta yi arba da nama ta sata ko ta dauki wani abun dadi ta boye a jakarta zan fi yarda, amman ko kudi bana saka ran Noor zata dauka a dan fahimtar da na yi mata na kankanen lokaci Noor ba zata san miye abun da ke jakarta ba, kuma mace makira ce Hafiz na ga hakan a zaman da na yi da Safeena da Yusura, baka iya ganewa kansu, yanzu idan ka ga yadda Yusura take min a gaban mutane ba zaka tana tunanin akwai wani abu na rashin so ko zaman lafiya a tsakaninmu ba, yanzu kuma har wani hali ta kirkira saboda Safeena ta zo gidan har dakina take kawo min abinci idan zan fita tace Allah ya tsare idan na dawo tace min sannu da zuwa, na fara tsorata da lamarin matar nan” Hafiz yayi murmushi. “Safeena ta zo gidan fa ka ce Kareem? Amman ban taba ganin mutumen da ya raina matarsa ba irinka” “Ba zuwa na yi da ita ba, kuma na gayyato ta na yi ba saboda na daina daukar wayarta ne ya saka ta zo da sunan ta zo min gaisuwa, amman dai na taka mata burki. So ni ina ganin ya kamata ka yi bincike ko kuma ka yafe mata ka rufe maganar kawai ba wai ka dauke mata kafa ba, kuma ka daina magana da ita a halin da take karkashin kulawarka. Ka ga duk yadda nake da Yusura bata so na bana sonta ba ma zaman dadi amman a haka idan na ga ta wuni bata fito shiryawa yara abu ba, ko kuma ban ji motsinta ba na kan leka na duba lafiyarta domin hakkinta ne da ya rataya a wuyana, please ka gyara” “Zan gyara, amman kamar yadda baka yarda Noor bata san komai akan samun maganin a jakarta ba ni ma ban yarda Aisha ta saka mata ba, na san wacece Aisha shekara nawa muna tare da ita, mace ce mai kirki mai mutunci” Kareem be sake cewa komai ba, domin baya son ya zafafa kasancewar ba shi da hujja kuma baya son Hafiz ya dauki abun ta wata sigar. Sai dai abun da be sani ba Hafiz ya gama fahimtar har yanzu akwai Soyayyar Noor a zuciyarsa hakan kuma ya saka shi jin kamar aurenta ba shi da amfani a gareshi. Sai bayan Sallah Magariba suka rabu da juna Hafiz ya nufi gidan Kareem kuma ya fito ya zauna a harabar kamar yadda ya saba domin baya shiga gida sai bayan Isha'i lokacin da yake tare da Safeena gidansa da suke badala yake tafiya sai kusan 11 ko 10pm suke rabuwa... A hanya yayi sallah Isha'i sannan ya shiga gidansa, yana faka mota yaransa suka fito da gudu suka tarbe shi sai ya daga su sama yana ajewa yana dariya. “Baku yi bachi ba” “Eh Daddy me ka siyo mana” “Ban siyo komai ba amman dai akwai chocolate a daki muje na baku” Ya kama hannunsu suka shiga ciki babbar ta rufe kofar falon, Yusura ta mike tsaye daga zaune da take. “Sannu da zuwa” “Yauwa Sannu” Yana rike da hannun yaransa ya haura sama suka shiga dakin, gaban maduni ya tsaya ya fara cire agogonsa akan Areef ya hau gado yayi tsalle ya haye masa baya yana dariya, shi ko yana juyowa ya fara masa chakulkuli sai dariya suke har shi gogan. Gurin da yake aje kayan dadin ya bude ya dauko ya mika musu. Yusura ce ta shigo dakin hannayenta a baya tana kallonsu. “Tine ku je falo zan yi magana da Daddy” Ya juyo ya kalleta, su suka sauka daga kan gadon suka fice daga dakin. Karasa ta yi kusa da shi ta dora masa abun da ta samu a aljihunsa kan gado. Ya kalli maganin da sabuwar robar ya kalleta irin kallon nan na me aka yi? Ita ma ta yi masa irin kallon ya aka yi suka zo aljihunka. Ya dan tabe baki “Ba nawa ba ne” “Su suka kawo kansu?” “Ni ban taba amfani da condom ba a rayuwata, da maganin da cdm din ba nawa ba ne, dalili ya kawo su” “Dalilin nake son ji” “Miye matsalarki da shiga hurumi har kina bincikar kayana? Ki tsaya matsayinki kar ki sake yi min haka” “Okay so kake na zuba maka ido ka lalace? Matan auren har gida suke zuwa nemanka? Ka ba su fuska na nuna musu ba ni da muhimmanci a gurinka?” “Babu wata alaka tsakanina da su, can you excuse me please...” “No idan wani abu ya faru yanzu ai ni za a zaga saboda Momy bata raye ni za a dorawa laifi” Da mamaki yake kallonta wato gata uwarsa. “Me ya same ki ne? Why are you behaving like this? Ba ma shiga hurumin juna, me ya canja yanzu” “Babu abun da ya canja, kawai duk abun da nake ina yi ne saboda yarana, kuma ba zan sake daukar wata karuwa ta shigo cikin gidan nan nemanka, ka tsaya can waje ka yi tun da ka lalata rayuwarka, ka dauki hakkina ga hakkin yara ga hakkin Momy ga hakkin Daddy ga hakkin Allah ga hakkin matan da kake lalatawa ga hakkin mazansu da yayansu kana zuwa lahira wuta a a saka ka kai tsaye...” Shi dai kallonta kawai yake har ta gama balbalin bala'in ta fice daga dakin. Because he's not a fan of argue. Juyawa yayi yana kallon kofar be taba aikata wani abu da ya shafi rayuwarsa ya ga Yusura ta fusata haka ba irin wannan, kuma ta nuna a fili sai wannan karon, and the most funniest part is yadda ta jero masa hakkin kowa a kai kamar ita zata kai shi wutar. Kai ya girgiza sannan ya shiga bandaki yayi wanka ya fito ya shirya cikin Pajamas. NOOR POV. Yadda nake kwana sati biyu da suka wuce haka na kwana a yau ma. Wato kwanan bakinciki da damuwa da kuka da kuma kadaici. Da safe na fito na gyara falon da be yi dattin komai ba na shiga kitchen na hada tea na fito falon na zauna ina sha. Muryar Aisha na ji tana yi ma Hafiz Allah ya tsare. Hakan ya saka ni mikewa tsaye na isa gurin windows din na bude sai na hango shi zai shiga mota ita kuma tana tsaye da murmushi a fuskarta sai hannu take daga masa. Har ga Allah bana son Hafiz kuma bana jin zan iya son sa ba shi kadai ba har zuciyata ba zata taba kaunar wani namijin ba bayan Zafeer amman tabbas ina jin zafi sosai yadda ya aje ni a karkashinsa amman ya kasa yi min inuwa kuma yana min ba ni muhimmanci a gurinsa. Ina kallonsa ya tuka mota ya fice daga gidan ba tare da ya shigo bangarena ba, na yi tunanin zai shigo ko da fada ne yayi min ya tambayi ina na tafi ba tare da izininsa ba. Kuka na yi har sai da numfashina ya fara sakerwa na kasa cin komai a wunin sai kuka. Sallah ma daker na yi saboda jikin babu karfi, I'm so hopeless babu mai taimakona, ko da zan mutu a wannan halin na kunci da nake ciki babu wanda zai kawo min dauki. A falo na yi sallah magariba ina sanye da hijab dina milk color na ji tsayawar motar Hafiz, sanin ba zai leko bangarena ba ya saka ban leka waje ba, kar na yi arba da bakinciki. Sai dai abun da ban yi zato ba ne ya faru, ganinsa na yi a falon kamar an jefoshi gabana ya shiga bugawa da mugun karfi ganin yayi tsaye a kaina yana kallona ni kuma na gagara cewa komai. “Ina kika je jiya?” Gabana ya fadi na gagara cewa komai sai hade yawu nake. “Gurin Kareem? Office kika same shi ko gida.?” Na sauke kaina kasa nan ma bana iya fadar komai. “Ke wai sai yaushe zaki yi hankali?” Na ji sanyi hawaye ya jika fuskata. “Ta so muje” Na dube shi da sauri. Kamin na yi wani yunkuri har ya mike tsaye, a dole ni ma na yi tsayen na bi bayansa sai ya juyo ya kalleni. “Je ki saka talkaminki” Na nufi gurin da talkamin suke na saka shi kam tuni ya fice daga falon ma. Ko da na fito ya tashi motarsa da kansa ya bude min front na shiga na zauna ya rufe sannan yaja motar muka fara tafiya, be kalli inda nake ba ni ma ban kalleshi ba sai sake saken nake a zuciyata ina zai kai ni? Me Kareem ya fada masa? Ina son na tambaya amman na kasa saboda bakinnya rufe min gam. Unguwarmu ya nufa yana ratsa gidajen dake ciki har ya isa kofar gidanmu, a nan na fahimci so yake ya hada ni da iyayena. Na kalleshi hawaye na min zuba. “Fita ki shiga gida, ki zauna sai na neme ki...” Ya fada ba tare da ya kalleni ba, na juyar da kaina dake rawa na bude motar na fita sai na yi tsaye na kasa daina kallonsa na kasa juyawa na shiga cikin gidan. Mun dauki mintuna a haka sannan ya miko hannu yaja gambun motar ya rufe yayi mata key ya bar ni a gurin tsaye cikin ruwan hawaye. Me kuma aka ce na ce? Yanzu kuma wane kalar laifin na aikata? Na zauna sai ya neme ni ya sake ni kenan ko kuma yaya? #KhadeejaCandyPAID PAGE 9️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Na kusan minti talati tsaye kofar gidanmu kamar wanda aka cewa shiga ki tararda hisabinki haka tsoron shiga gidan ya kamani, domin na san waye mahaifina. Amman ba ni da wani gurin da ya fi gidan ina zan je? Ai ba ni na kawo kaina ba shi ya kawo ni. Cikin kasala da fargaba irin na wanda ya rasa makoma na saka kafata a gidan, duk yadda nake son hana hawayena zuba kasawa na yi. Sai kuma na yi rashin sa'a Baba na tsakar gidan yana alwala, ban yi sallama ba domin bakin har lokacin a rufe yake. Baba ya hasko ni da fitilarsa mai haske. “Wa nake gani kamar Norriya?” Tafiya kawai nake cikin gidan na kasa Cewa komai. “Lafiya?” Na durkusa a gabansa. “Wani abu ne ya samu Hafizun?” Na girgiza kai. “Toh me ya faru?” Hana ta fito daga daki tana kallona cikin tashin hankali. “Cewa na zauna sai ya neme ni” Fitilar dake hannun Baba ta subuce ta fadi kasa. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un, daman ai sai ba ke ba Noor, yanzu duk irin abubuwan da mutunen nan yayi min yayi miki sai da kika kai shi makura? Tafiya kika yi kina masa shashanci da sakarcin na ki ko? Har ya gaji yanzu ya koroki gida” Na matsa baya da sauri jikina na rawa domin fadan da Baba yake min irin na son duka ne. “Yaushe aka yi auren da zaki biyo dare yanzu ki ce wai yace ki zo gida?” Na bude baki zan yi magana ya daka min tsawa ya cire talkaminsa ya jefani da shi. “Ban son jin komai daga bakinki, marar mutunci daman ai na san sai kin masa shashanci, kina kallon yadda rayuwa take a gidan nan kin samu mai rufa miki asiri ne shi ne kika fara masa rashin kunya ko? Saboda ya sake ki ki auri Zafeer ke ga ki shim mai ruwa uku shashasha, sakinki yayi?” Na girgiza kai. “To tashi maza ki koma dakinki, ina nan ina jindadi na samu suruki mai dauke mana komai shi ne zaki fara watsa mana kasa a ido? Ni daman sai da zuciyata ta raya min anya ba kina masa rashin mutunci ba ne, in ba haka ba da yanzu ya gyara mana gidan nan amman shiru, ashe kina can kina nuna masa rashin tarbiya, mai kashin tsiya so kike mu koma rayuwarmu ta baya ko? Ke yar zamani, minti biyar ban yarda ki kara yi a gidan nan ba, koma dakinki gobe zan zo na ji me ke faruwa amman Wallahi ba zaki kwana gidan nan ba, wato halin uwarki zaki dauka na rashin hakuri ko? Ko kuma so kike ya sake ki ki dawo ki sake zaunawa ke da kanwarki a daki daya? Wawuya marar hankali, wato ki zaki nunawa wai ba zaki yi zaman aure ba ko? To na fiki zama dan tasha... ” Ya karasa yana daukar butar da yake alwalar da ita ya jefa min. Na tashi da sauri na fice daga gidan ina kuka, Baba be saurari izurina ba ya koroni daman na san hakan zai faru, da na fito sai tashin hankalin yayi min yawa na rasa ina zan je, na koma gidan Hafiz din da ya kawo ni gida yace na zauna sai na neme ni ko kuma na tafi gidan Mama? Ita ma koroni zata yi. Haka na bi hanya ina tafe ina hawaye har na isa titi, wata zuciyar na ce min na tafi gidansu kawata Zainab na kwana, domin ba ni da kudin abun hawa ma balle na koma gidan na san kuma ba zai ba ni ba, wata kila ma na samu ya fadawa mai gadinsa cewar kar a bar ni na shiga cikin gidan. Juyowa na yi na dawo cikin unguwarmu na shiga gidansu Zainab, Umma na ganina ta san ba lafiya ba, kamin Zainab tace min komai Umma ta fara tambayata lafiya. “Umma Hafiz ne yace na zauna a gida sai ya neme ni, na zo kuma Baba ya kore ni, na san idan na tafi ma Mama ba zata saurare ni ba, ban san inda zan je ba” “Wani abun kika masa?” “Ban masa komai ba Wallahi ban masa komai ba” “Aa Noor ba zai yiyu haka nan kawai yace ki tafi ki zauna a gidanku ba, sai kin masa laifi, Allah yasa dai ba Zafeer kika saka a zuciyarki ba, kar soyayyarshi ta hana ki zaman aure, ki kama kanki Noor ki natsu, yaushe aka miki auren da har za ace an fara samun matsala irin wannan?” Na yi shiru domin ba kowa zai yarda da ni ba. “Kin ga ni ba zan baki mafaka ba, mahaifinki ya koreki wace ni na baki gurin zama? Ai zai ma iya ci min mutunci ko kuma a ce saboda ni ba uwarki bace yasa na yi haka, ki yi hakuri ki koma dakinki ki bawa mijinki hakuri ku zauna, shiyasa ma na hana Zainab tafiya gidanki kar wani abu ya faru ace ita take hure miki kunne, ki yi hakuri ki koma dakinki Noor” “Tohm...” Na amsa kana na juya domin bata bar ni na zauna ba ma, haka na fito daga gidan ina hanya Zainab ta tarar da ni ta ba ni 500. “Mama tace ki hau Napep, kuma Noor idan ba zaki iya komawa gidan kai tsaye ba, ki tafi gidan iyayensa ko kuma wani dan'uwansa wanda kika san yana jin maganarsa, sai a kira shi a yi masa magana kinji” “Ban san gidansu ba, be taba kai ni ba” “Ko gidan wani abokinsa ba kisa ni ba?” “Na sani amman hakan zai iya bata masa rai, jiya naje can na fada masa amman be yi komai ba, wata kila shiya saka yau na ce na dawo gida na zauna” “Idan kin tafi kice ya fada miki gidan iyayensa ki tafi, ba wai dole shi zai masa magana ba, kuma Noor na san halinki da rashin jin magana dan Allah ki zauna lafiya” Na yi murmushi ina jin ina ma ace ni ce a matsayinta. “Na gode Zainab” Ta tsaya a gurin har sai da na samu Napep na hau sannan ta juya. Kuka ne abun da nake yi har mai napep din ya isa kofar gidan Kareem. “Allah yasa lafiya kike wannan kuka ko mutuwa aka yi?” Ban ce masa komai ba na mika masa dari biyar din na fita Napep din ina kallon gate din gidan ban san me zan sake ce masa ba. Ina ta zuwa masa da matsalata, waya sani ma ko hakan ya zama sanadin mutuwar auren nawa gaba daya. Sai dai ba ni da wata mafitar bayan wannan, a gaban gate din na duka ina kuka sosai. Da rarrafe na isa gate din na kwankwasa, babu jimawa mai gadin ya bude ya leko. “Waye?” Na share hawayena na mike tsaye. “Ni ce wadda na zo jiya, Kareem yana nan?” “Eh yana ciki” Ya bude na shiga ido a kumbure hancina n yaji saboda majina da gugar da ya sha, fuskata ta yi ja sosai. Kai tsaye na nufi cikin gidan cikin rashin sakewa da tunani kala kala a raina, damuwa ta saka na manta waye matar Kareem, na manta cewar huruminta na shigo domin mijinta. Na kwankwasa kofar falon ta bude min ni da ita muka tsaya kallon juna. “Ke ce?” Na daga mata kai. “Kareem yana nan?” “Eh yana nan shigo” Na goge gudun hawayena na shiga falon na tsaya daga gurin kofar ina kallonta. “Ina son magana da shi ne dan Allah” “Okay ina zuwa bari na kira shi” Ta juya ta nufi wani gurin da nake kyautata zaton kitchen ne. Bata ji ba ta fito nufo gurin da nake tsaye. “Ki shigo ki zauna mana bari na kira shi” Ba tare da tunanin komai ba na shigo kamin na zauna ta ware hannunta ta buga wani abu mai mugun karfi a kai, ban gama tantance miye ba na sake jin saukarsa a wuyana, wani irin jiri ya dauke ni na soma ganin ta zame min biyu kamin idon ya rufe... *** *** *** Babu ihu babu kokarin kare kai Noor ta yi kasa idon suka rufe, gefen da ta buga mata mociyar kuma jini ya fara jika hijabin har ya zubo kasa. Da sauri Yusura ta saki muciyar ta matsa baya jikinta ya fara rawa, me ya kaita? Me yasa ta aikata? Ina tunaninta ya tafi haka? Sai kuma ta matsa ta taba Noor ta ji bata motsi ta sake matsawa baya ta zauna kan kujera hankalinta a tashe jikinta na rawa. Kaminnta tashi da sauri ta haura sama. Dakin Kareem ta shiga yana sanye da multicolours din Pajamas dinsa hannunsa rike da books din Rules of the Journey. Daga kishingiden da yake ya dago kai ya kalleta ko'ina na jikknta rawa yake tashin hankali a fuskarta karara. “Ya.. Yarinyar da ta zo jiya ce ta dawo yau” Kareem ya rufe littafin yana kallonta hankalinsa kwance. “An samu akasi na buga mata abu ta fadi” Wani irin tsalle ya daka ya sauko daga kan gadon. “What.... Me yake damunki? Why?” Ya fice daga dakin da sauri sai ta bi bayansa kamar zata yi kuka. Kareem ya sauka kasa ya karasa gurin da Noor take kwance cikin jini. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un, Me kika aikata haka Yusura? Baki san me ya kawo yarinyar nan gidan nan ba, ban san halin da take ciki ba kawai ki kara mata da wannan?” “Ta mutu ne?” Yusura da ta kasa karasa saukowa ta tambaya cikin kuka. Kareem ya saka hannunsa ya cire Hijab din Noor ya taba wuyanta ya cire dankwalin kanta ya daure mata kan dake zubar da jini sannan ya tashi ta sauri ya haura sama ya dauko keys dinsa ya fita ya janyo motarsa ya kawo kusa da entrance din ya shiga falon ya dauko Noor da bata san inda take ba ya saka ta bayan motar ya shiga driver side ya ja motar sai asibiti. Gado aka bata shi yayi mata duk wani treatment da ya kamata, ya saka mata drip sannan ya lalaba aljihunsa ya sai a lokacin ya tuna be zo da wayarsa ba. “Oh nikan matan nan son hada min wuta...” Ya fada yana kallonta. “Me ma ya sake fito da ke Noor?” Tambayarta yake kamar ance masa zata iya amsawa. Dakin ya fita be bar asibitin ba sai da ya tsabtace kansa sannan ya shiga motarsa ya koma gida. Yana shiga falon Yusura ta mike tsaye tana kallonsa. “Tana raye?” Wani mugun kallo ya watsa mata. “Kusan wannan ne karo na biyu da kike kokarin illata yarinyar nan, wannan ya zama na karshe, wacan karon kamin ta yi aure ne har ina fada mata kawai dai an samu akasi ne, ba wai dan kishi ba, yanzu kuma ban san me ya zo kanki ba...” Ta matsa kusa da shi. “Yanzu din ma akasi ne, gobe da jibi din ma akasi ne matukar bata dauke kafarta daga gidan nan ba, kusancinta da kai yana kusanto maka da mutuwa ne kai da ita” “Idan kika kasheta zai ba ni mamaki, domin baki da wani dalili na aikata hakan. Kashe ni ba zai bada mamaki ba, tun da na san ba ki so na, ko akwai abun da ya canja?” “Babu Kareem babu, babu abun da zai canja har gaban abada...!!! Ko a mafarki bana fatan ko a lokacin da kake da natsuwa balle yanzu da kake bibiyar matan aure ciki har da matar amininka...” Ta fada da karfi sannan ta juya, fisgota yayi ya dawo da ita. “Babu wata alaka tsakanina da Noor, idan har zan kulla wata alaka makamanciyar wadda kike zargina da ita, to da zan aureta ne na aje ta a gidan nan under the same roof mu rayu har abada ni da ita, sai dai kuma babu irin wannan sha'awar tsakanina da ita” “An fada min ai, kun yi soyayya sai kuma ka saka abokinka ya aureta deal ne?” Sakinta yayi yana murmushi. “Haba ke kuwa taya Kareem zai yi soyayya da wata yarinya, yana da damar aurenta kuma sai ya ki aurenta ya saka abokinsa ya aure ta? Daga baya kuma ya zo yana bibiyarta? Wane irin ƙidahumi ne ni? Ai da abun da aka fada miki ne ya faru to sai dai na aurota na kawo nan mu sha soyayya” Abu ta hade da karfi ta juya ta haura sama ta barshi a gurin tsaye. Ta wani bangaren baya ganin laifin abun ta aikata domin gidanta suka shigo kuma neman mijinta, ta gurin da abun zai daure masa kai ace tana kishinsa domin abun da ake so ake kishi, shi kuma be saka ran samun haka daga gurin Yusura. Isakar bakinsa ya busar ya nufi dakinsa ya wayarsa ya dauka ya kira Hafiz. “Hello...” “Barrister kana gida?” “Ina gida lafiya?” “Zaka iya fita waje mu yi magana” “Okay....” Shiru na 2 minutes ne ya shiga tsakani kamin Hafiz ya amsa daga dayan bangaren. “Ina jinka” “Kun sake yin fada da Noor ne?” “Daman ba fada muke ba, kawai dai na turata gidansu ne yau?” “Saboda me?” “Tana bukatar a koyar da ita zamantakewar aure Kareem, ba zan Boye maka ba na fara nadamar auren yarinyar nan!” “Subhanallahi, to maybe wani abun ya faru a gidansu ko kuma bata tafi gidan ba, ta zo gidana by mistake Yusura ta fasa mata kai yanzu haka dai tana asibiti” Hafiz yayi shiru kamar ba zai ce komai ba. “Dan Allah kaje ka sameta kuma ko miye a tsakaninku ka yi hakuri mana Hafiz, hankalin Namiji baya zama daya da mace, kuma san halin mahaifin yarinyar yana daga cikin dalilin da ya saka ka aureta saboda ka tsamota daga kunci, to miyasa ba zaka jure ba kana lurar da ita har ta fahimta, ba mamaki mahaifinta korarta yayi ta rasa gurin zuwa ta zo nan, ni kuma ban ma sani ba sai fitowa na yi na samu Yusura ta yi mata aika aika, kuma kai ya kamata na kira domin responsibility dinta yana kanka as her husband don't misunderstand the issue please” “Tana ina yanzu?” “Tana asibitinmu, emergency room 44, please ka sassautawa yarinyar nan Hafiz duk yadda kake tunanin hankalinta be kai can ba, a yanayin yadda na fahimta ta tashi a wani yanayi ne na rashin dace da iyaye shi ne musabbabin komai, idan ka hada mata zafi iyayenta suka hada ma za ku iya sakawa ta kamu da depression domin bata da mai rarrashinta bata san gurin da zata tafi ta ji sanyi ba, ta yi kankanta ace ta fara samun matsalar aure tun a yanzu, and idan bata samu kwanciyar hankali a gidan ka ina zata samu? Already ta rabu da wanda take so, idan ta rabu da kai iyayenta za su iya juya mata baya, idan a gidanka bata jin sanyi kashe kanta kuke son ta yi? Kai da kanka ka ce za a iya koya mata son wani, to ka koya mata mana, ka nuna nata gurin da illar abu yake da sannu zata gyara” Hafiz ya ki ce komai ba, sai wani cika zuciyarsa take duk abun da Kareem yake fada shi wani abun yake hangowa can dabam. “Good Night” Kareem ya kashe wayar ya jefar kan gado ya sauke dogon numfashi. “Poor girl” Ya furta, ya zauna bakin gadon yana jinjina kai. NOOR POV. “Good Morning...” Na ji wata matar da ban taba arba da kalar fuskarta ba ta fada tana yi min murmushi. Yunkurin tashi na yi zaune sai ta rika ni na zauna na sake dubanta da idanuwa da ba su gama budewa ba. “How are you feeling now?” Na daga mata kai ina jin kamar an dora min wani dutse a gefen kaina saboda nauyin da yayi min. Hannu na kai na taba sai na ji an daure gurin, gefen wuyana ma an saka min wani abu a gurin sai ciwo yake min. “Ya jikin na ki?” “Da sauki” Na amsa ina kallon dakin da ban san lokacin da aka kawo ni ba. Gashi babu kowa a kusa da ni sai wannan nurse din da ba musulma ba domin sakar cross ce a wuyanta sai gashin doki da ta dora. Ta taba jikina ya cire robar ruwan da be kare ba sannan ta yi rubutu akan files din dake hannunta tana min tambayoyi, sunana umguwata ina da aure ko babu sai kuma number wayar Mijina ko ta mahaifina, da alama dai sabon file take bude min a yanzu. Sai da ta gama sannan ta saka hannunta aljihu ta ciro wata takarda ta miko min. “Ga wannan mijinki yace idan kika tashi a baki” Na mika hannu na karba, a gabanta na fara warware takardar har na bude. “A yau 2 ga watan 6 ni Hafiz Abdullahi na saki Matata Noor saki daya” Shi ne a rubuce, gashi sunana da nasa ne a rubuce balle na ce kuskuren fahimta aka yi aka ba ni abin da ba nawa ba. “Wayyo Allah.. Na shiga uku na lalace, wayyo ni Allah me yasa Hafiz zai sake ni yanzu na shiga uku, yanzu ina zan je? Wayyo Allah... Baba kashe ni zai yi, yanzu korata za su yi, na shiga uku” Na kalli matar ina kuka mai taba zuciya. “Dan Allah ki kira min shi” “Ya riga ya tafi, but bari na kira Doc abokinsa ne ai sosai” Ta fita dakin, sai na sauko daga kan gadon i don't even care about the pain haka na zube kasa kaina ya sake buga da gadon asibitin ina wani irin kuka, domin na san karshena ya zo, matar bata dade ba ta dawo ta miko min waya. “Ga Doctor zai yi magana da ke” Na karbi wayar da sauri na kara a kunne na saka hannu na dafe. “Noor sakinki yayi?” “Ya sake ni Kareem, rayuwata ta kare Baba zai iya tsine min ma, ba za su fahimta ba, dan Allah ka taimaka min ka ba shi hakuri, ka ce yayi hakuri ya maida ni gidansa ya yafe min, ka ce masa zan zauna a haka ba zan sake kai kararsa wani gurin ba, Kareem ka ba shi hakuri dan Allah ya hakura ya maida ni...” Ina maganar ina kara matse wayar a kunnena ji nake kamar yana tsaye a gabana ne na kama kafafuwansa na bashi hakuri, domin ni kadai na san halin da zan shiga a sakin nan da yayi min. “Ba zan ba shi hakurin ba” Ta cikin wayar Kareem ya daka min tsawa ya kashe wayar. Na kalli matar da bana iya ganin fuskarta a yanzu saboda hawaye ya tare ko'ina na idona. “Ya kashe... Ya kashe... Sun ruguza min rayuwa, sun raba ni da mai so na tsakani da Allah mai kaunata mai fahimtata mai tausayina, yanzu kuma sun hada ni da mahaifina shikenan rayuwata ta kare wayyo Allah na ni Khadija, Allah ba ni da gata sai na ka...” Nurse din ta dafa ni. “I'm sorry... Please take heart” Na kwanta jikinta ina kuka sosai kamar zan mutu, ni kadai na san waye mahaifina ni kadai na san halin da zan shiga. Da sauri na dago daga jikin matar mai sanyin hali na fara share hawaye, so nake na tafi na samu Hafiz a duk inda yake na ba shi hakuri ya maida ni gidansa... #KhadeejaCandyPAID PAGE 1️⃣1️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ KAREEM POV Fuskarsa a hade yana tsaye gaban madubi yana kokarin saka agogonsa Yusura ta turo kofar dakin ta shigo. Be dago ya kalli kofar ba amman hakan be hana shi fahimtar ita dince ta shigo dakin ba. Tsayawa ta yi nesa da shi ita dai fuska babu annuri ta ce. “Ina kwana?” “Lafiya Kalau” Ya amsa a taikaice sannan ya fuskanci madubin da kyau ya dauki turare ya fara fesawa. “Ka ce zaka yi shawara, zaka duba lokacin da ya dace ka aiwatar da abun da zai bawa kowa yanci a tsakaninmu, har zuwa yaushe ne Kareem” “Abokiyar shawarata wadda ta bani shawarar aurenki ko na ce umarni bata duniya, amman zan yi shawara da Daddy tukuna” Ya danna abun da ta ji yana taso mata a zuciya. “Har zuwa yaushe kenan? Tsawon shekarun da muka yi da kai ina numfashi ne cikin matsuwa, ina ta jiran ranar samun yanci” Kwalbar turaren ya aje ya juyo ya kalleta. “Na fiki shiga kangin na takura da kunci, da kin san matsalolin da aurenki ya janyo min wata kila, kin shiga daki kin rufe kanki kin yi kuka, Yusura na rasa natsuwata, na rasa farinciki, rayuwar da nake buri ko mafarkin yi aurenki ya ruguza ta, ba ke kadai ba ce a dakin damuwa, ni ma yancin nake nema, i deserved happiness too ba kullum bakin ciki ba, so please karki matsa komai a sannu yake zuwa, kuma zan fi jindadi idan kika daina shigowa dakina kamar yadda kike yi tun farkon zamanmu, bincikar kayana ko bibiyar rayuwata ba na ki ba ne. And ki daina biyo ni har daki da abinci, a dinning ma ya isa idan ina ra'ayi zan ci a can... Please excuse me... ” Ya zagayeta ya fice daga dakin, binsa ta yi da kallon ita kadai ta san yadda take danne zuciyarta take rayuwa da a gidan, amman yau ya kalli idonta ya fada mata magana son ransa. “You got to be kidding me... I'm doing all this saboda na sauke hakkina da Allah ya dora min, waya fada maka a cikin dadin rai ko neman kauna nake? I need space...” Ita kadai take magana da kanta a lokacin da ya dade da fice daga dakin, so take ta kyautata masa kamin ta bar gidan, tun a wacan daren da Safeena ta zo gidan, wani bangare na zuciyarta ke raya mata wata kila saboda rashin samuwa kulawar da ya dace ne ya saka shi tunanin aron hannu ko kuma ma aron gaba daya, tana jin kamar idan ta mutu Allah zai tambaye ta ko da kuwa bayan ta bar gidan ne. But what happened yesterday ya canja tunaninta idan rashin samun kulawa ne ya kai shi ga kula Safeena a yadda take zargi, to ita wannan Noor din fa? Bayan abun da ta kama a aljihunsa wadda ta hango Noor din tana hannanta masa ga kuma abun da Aisha ta fada mata. Now ta ji kamar ba zata iya tarar yakin ba, ba zata iya rumgumar wani dacin ba bayan wanda take ciki. Takowa ta yi ta fito daga dakin ta shiga nata dakin, arba da ta yi da hoton yaranta biyu like a bango ya tsumata. “Rabuwar ita kadaice mafita, ita kadai ce maslaha a gurina, nesanta da Kareem shi ne burin da na dade ina binnewa a zuciyata, dakun mutuwar Momy da nake a baya duk saboda samun yanci ne...” Ya zauna kan gadonta tana kallon hoton hawaye na sauko mata. “Yanci irin na ya mace mai burin auren wanda take so, yanci na rayuwa a karkashin inuwar wani namijin dabam da zuciyata zata yi na'am da shi ba Kareem ba, Wallahi kullum da wannan bakinciki nake kwana da shi nake tashi. Momy ta hada wuta da ruwa ne ba tare da tunani ba, bama haduwa da juna, ba mu dace da juna ba, dan Allah ku yafe mini” Ta kwanta saman gadon tana hawaye, tana jin kaunar yayanta domin babu ruwansu a cikin matsalarsu, sai dai kuma Kiyayyar Kareem ta fi soyayyar yaransa karfi a zuciyarta. *** ***  *** Tuki yake da hannu daya a lokacin da wayarsa ta yi ringing. Sai da ya kalli mai kiran sannan ya daga ya sakata a speaker. “Hello” “Doctor Ka fito gida?” “Eh ya aka yi?” “Wani dan abu na aikata” “Na me?” Barrister ya sauke ajiyar zuciya ta ciki wayar sannan ya ce. “Na saki Noor..!! Na san ba abu ne mai dadi ba, but ina ganin kamar hakan zai fi zame mana mafita, saboda akwai abubuwanta da ban gamsu da su ba, kuma ina ganin kamar ba zata iya canjawa ba” Doctor ya tabe baki ya kalli ne mirror sannan yayi overtake yana tabe baki. “Okay.. Daman aure rai ne da shi, na wasu ya kan dade na wasu kuma be dade ba, Allah yasa hakan shi ne mafita alheri, ya baka zaman lafiya da matarka, ita kuma Allah ya bata wanda ya fika ya dace da ita..” Hafiz yayi shiru ya kasa amsa da Ameen kuma ya kasa sake wani furucin, all what he expected Kareem ya fada hakan da ka yi ka yi daidai or no baka yi daidai ba. Sai dai kam be ji haka daga gurin abokin shawararsa ba. Kareem ya kashe wayar jin Hafiz be ce komai ba kuma be yanke kiran ba. Tuki yake cikin natsuwa har ya ratso cikin unguwarsu Noor, a gaban gidansu ya faka ya bude motar ya fito rike da wayarsa. Nabil ya kira yana dagawa ya ce. “Ranka ya dade” “Kana gida?” “Eh ina gida ranka ya dade” “Fito ina waje” Before Kareem yayi blink Nabil ya fito ya fito da saurinsa. At that time ne Kareem ya daga kai yana kallon kofar gidanta data kone kana ganin gidan zaka san an yi gobara. “Oga Allah yasa ba wani laifi na yi ba” Kareem ya mika masa hannu da suna gaisawa amman Nabil ya ki ya karba saboda yana jin kamar kuskuren gaisawa da mai gidansa a lokacin da yake karkashinsa, shi kuma yake samansa sosai. “Ka yi laifi zan biyo ka har gida? Me yasa kullum tunaninka ka yi laifi ne ko dai akwai laifin da kake min ne a restaurant ban sani ba?” Nabil ya shafa kansa yana dariya. “Aa Wallahi oga, na ga yanzu Noor bata nan balle ace ita ta janyo min wani abun a gurinka” Kareem be biye mishi da maganar ba sai ya tambaye shi yaushe aka yi gobara a gidan. “An yi sati uku yanzu” “Subhanallahi, Allah maida alheri na zo gurin mahaifinku ne yana ciki?” “Eh yana ciki kasan safiya ce yanzu, be isa fita ba” “Good ka yi masa sallama, amman kamin nan me yasa kullum nake samunka a gida baka karatu ne?” “Na fara kuma abun ya zo da dan nauyi sai na aje sai nan gaba kuma” Nabil ya fada yana sosa kansa cike da kunya. “Allah ya taimaka, sallamo shi” “Ameen ranka ya dade” Nabil ya juya ya shiga cikin gidan, nan ma babu jimawa Baba ya fito yana gyaran hula ganin Kareem ya saka shi washe hakora ya mika masa hannu biyu suka gaisa. “Baraba da zuwa, baka shigo ba kake zaune a waje” “Ba sai na shiga ba, magana ce kawai na zo da ita zamu iya yi a waje ma Baba” “Toh Allah yasa dai lafiya” “Lafiya Kalau, Irin na amsu lafiya ba irin na masu matsala ba, Baba na zo da magana ne mai nauyi kuma daci sai ka jure” “Kar ka ji komai fada min ko minene kai tsaye” Kareem ya sauke ajiyar zuciya. “Baba jiya, ko kuma ma na ce kamin jiyan Noor ta samu matsala da mijinta wanda amini ne a gurina, kusan ma ni ne dalilin auren domin sanadina ya san ta ni kuma na san ta sanadin danka Nabil” “Haka ne, ai ta zo nan na korata bana son sauraren komai daga gareta, domin na fahimce take takenta so take ta kashe auren, yaushe aka yi auren ma? Fisabillilahi, a yau ma nake da niyar tafiyar gidan shi Hafizun na ji rashin mutuncin da take masa, domin komai aka ce Noor ta yi bana musu yarinya ce da bata da jin magana sam” “Amman ka bincike me yasa ta zo gida?” “Bana bukatar ji, ai ita mace baiwa ce namiji ko dukanta yake be kamata ta yi yaji ba ko ta zo gida kawo shedu idan na bata wannan kofar kamin ka ankara kashe auren zata yi” “Zaman lafiya be tsawaita aure, tashin hankali be gajarta aure, ko ya kashe rai ne da shi ko ana zaune lafiya mutuwa yake, idan lokaci yayi, wani kuma ga tashin hankali amman auren ya ki mutuwa saboda lokacin rabuwar be yi ba, da dadi da ba dadi as long as auren yana raye za a zauna” “Haka ne, amman Noor ba a nuna mata wannan, yarinya da bata da tunani babu natsuwa a tare da ita” “Amman ko minene ya kamata ka saurari damuwarta, ka aura mata wanda bata so at her young age kuma ta yarda ta aureshi, yanxu kuma ta zo da matsala ya kamata ka aurareta, mace bata da gidan da ya wuce na uba a duniya idan aka cire gidan mijin, wani bangaren ma gidan uban ya kan fi na mijin, domin yanzu da ya korota gidan ubanta ta doso, da namiji ne shi zai yi korar ko kuma ya nemi wani gurin ya fake, irin haka yana saka rayuwar mace ta lalace” “Wato duk abun da za a fada maka ba zaka gane ba, ita Noor dabam take ta sauran yaya, kuma ka duba yadda abokin ka yayi hidima da mu, ace wai Noor ta kwaso jiki ta zo gida ai be kamata ma na saurareta ba” “Ina ganin ku kuka haifi Noor a hannunku ta girma ta yi wayo, amman ko ku din ba ku fi ni fahimtarta ba, ban sani ba ko dan ina kallonta a wani yanayi ne da ku ba a baka kuke kallonta ba” “Ni fa na haifi noor na san halinta gaba da baya” Kareem ya aje numfashi da karfi. “Ko ma dai minene yanzu, Baba ina son ka karbi wannan kaddarar, dan Allah ka yi hakuri ya karbi Noor, ni kuma zan shiga na fita na ga na yi abun da ya dace” “To wai sakinta yayi ne ko kuma me?” “Sakinta yayi, ni kaina ban san abun da ya hada su ba, amman dai yanzu haka Noor din tana asibiti saboda buga mata abu da aka yi a kai ta ji ciwo sosai” “Yayi daidai ai kara da yayi mata duka, daman Noor bata san arziki ba, wato ni zata watsawa kasa a ido ko? Aure ko wata daya be yi ba ta an sakota ta dawo? Oh Allah na gode maka da ka yi min wannan kyautar, yarinyar nan ban da bakinciki babu abun da take saka min tun da aka haife ta, yanzu ina murna na aurar da ita na huta ita ma ta huta, sai kuma yanzu na ji wani labarin na dabam? So take fita sallah cikin jaama'a ma ya gagareni?” Kareem yayi shiru ba tare da fada masa dalilin dukan ba, ko fayyace masa cewar ba Hafiz ne yayi ba matarsa ce ta yi mata duka a rashin fahimta. Sai kawai ya dora da “Hakuri zaka yi Baba, komai zai wuce” Baba yayi baya baya ya jingina da ginin gidansa, gaba daya furucin saki da Kareem ya furta ya fi jefa Baba cikin damuwa, duk wani buri da hangen dafgen da Baba yake a auren Hafiz da Noor ta yi ya sha ruwa. “To wai saki har nawa yayi mata ne?” “Daya ne ina zaton ba zai wuce haka ba, ni dai abun da nake so daga gurinku shi ne hakuri ku karbeta, zan binka komai kuma da yardar Allah zata koma dakinta amman dole sai ka yi hakuri Baba” Kareem ya fada ne kawai saboda ya samawa Noor matsuguni a gidansu ba wai dan yana da niyar yin wani abun akan auren ba. Be ji zai iya sake tuntubar Hafiz ma da maganar ba balle har yayi ruwa da tsaki Noor ta koma gurinsa. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un, wannan yarinya ba zata tana canja hali ba, to sai ta zo ta zauna ai ta ji idan zaman gidan dadi ne da shi, sakarya kawai marar hankali” Kareem be ce komai ba ya bude motarsa ya dauko 50k ya mikawa Baba. “Baba ga wannan ayi chefa ne, ina mai kara baka hakuri akan abubuwan da suka faru, kowa baya wuce kaddararsa. Ka yi hakuri dan Allah yanzu haka Noor tana asibiti, ita kanta tana cikin tashin hankali na abun da ya faru” Baba ya saka hannu biyu ya karbe kudin ya jefa alJihu sai dai har lokacin damuwar bata bar fuskarsa ba. “Toh dole ai zai hakuri, yaran zamani ne duk yadda zaka fada musu abu ta bayan kunnensu yake bi” “Allah ya kyauta, zan tafi zan samu abokin nawa sai mu tattauna” “Toh an gode, ka ba shi hakuri dan Allah, na san halin Noor zata iya komai, ka ba shi hakuri ita kuma In Shaa Allahu za mu gargadeta” “Tohm” Kareem ya shiga motarsa yayi mata key ya juya ya fice daga unguwar. NOOR POV. Duk yadda na yi kokarin tafiya sai matar ta sha gabana da kalamai ta hana ni fita. Ina zaune har kusan sha daya na rana ina ta tunanin mafita, na sake kiran Kareem na masa magana ne ko kuma dai idan na samu damar fita na tafi kai tsaye gurin Hafiz na ba shi hakuri. Karar turo kofar dakin ne ya saka na daga kai na kalli kofar arba da na yi da fuskar Aisha ya saka ni jin kamar an kara min ciwon dake jiki even though ba ni da tabbacin tana tare da Hafiz ne ko akasin haka. Cooler abinci ce a hannunta Ina zaune ta karaso ta aje kayan abinci cikin tausayin da yanzu na tabbatar na makirci ne Aisha ta zauna a kujera tana kallona kamar zata fasa kuka. “Noor ya jikin na ki?” Na dauke kai na kawarta da fuska ba tare da na amsa ba. “Noor rai ne ya bace haka? Ki yi hakuri da abin da ya faru, ni kaina ban jidadi ba, Wallahi be fada min ba sai yanzu da zai fita, shiyasa na yo rushing na zo dubaki ya jikin” “Bana bukatar dubiyarki, dan Allah ki tashi ki tafi” “Ikon Allah ni miye nawa a ciki Noor? Dalilin zuwana fa so nake a gyara abun nan kamin ma familynsa su sani” Na juyo na kalleta. “Duk halin da na shiga a yau ke ce sila, gaba daya kin rikita min tunani kin dasa min abubuwan da babu a zuciyata, daga baya kuma kike daure ni da su kina cutar da ni, bana son ganinki Aisha” “Hmmm Allah sarki, an hure miki kunne ko? Ke yarinya ce baki san miye duniya ba, amman ni kauna nake nuna miki saboda na rike ki ne tsakani da Allah” “Karya kike yi, kina munafurci ne kawai kina ke din ta kwarai ce alhalin ba haka ba ne, to yanzu ya sake ni hakan be wadatar dake ba sai kin biyo ni har nan?” “Alheri ne ya kawo ni ba sheri ba, ban jidadin yadda kike jefata da zargina da abun da ba hali na ba, wata rana zaki gane gaskiya” Ta mike tsayeta fice daga dakin. Wasu hawaye masu zafi ne suka sauko min, na sani ko da zan fadi kasa na yi birgima na roki ta ce Hafiz ya maida aurensa da ni ba zata yi hakan ba, domin ita ce silar lalacewarsa, aikata hakan kuma raina kai ne a gurinta da janyowa kai gori. Ban saka tsamanin zuwa kowa ba domin ba zan iya tunkarar mahaifina da takardar Saki ba, kamar yadda na san Mama ba zata saurare ni ba, babu wanda zai duba ni, babu wanda zai yarda da ni ko da kuwa ina da gaskiya. Sai dai abun da ya fi komai yi min ciwo shi ne, me yasa Hafiz zai aureni alhalin ya san yana son matarsa kuma ya san ba zai iya adalci a tsakanina da shi ba, ba zai iya tausaya min ba. Misalin karfe daya ina zaune a dakin shiru Gwaggo Saude tare da kanwarta suna shigowa bata duba halin da nake ciki ba ta rufe ni da fada kamar wadda bata da gata, sai kanwarta ce take dan tare min tana cewa ba a bincika ba wata kila ni ce mai gaskiya. Ban san waya fada musu ba ban san ta ina suka ji ba maganar sakin ba domin ban yi maganar da kowa ba bayan Kareem. Haka na yi kwana biyu a asibitin a duk tsawon zaman da na yi Hafiz be leko ba, daman me zai saka ya leko ni bayan ya datse igiyar data hada, mahaifiyata kam ina jin bata da labarin komai sai dai abun da ya daure min kai shi ne rashin zuwa Ya Nabil da Hana duba ni, haka ma Baba be zo ba, Kareem din ma da matarsa ta yi min illa be leko ba ko sau daya be taba shigowa ya duba ni ba. A zaton su raunin da na samu Hafiz ne yayi min duka ni kuma ban damu na fada ba domin ni na kai kaina fadar zai kara janyo min karin wani tsanar ne ko fadan. Idan suka tambaye me ya faru tsakaninmu sai na ce babu komai ban masa komai ba, na samu kaina da nauyin fadar dalilin asalin fada na samun robar c**mdom da maganin planning a jakata, a lura da na yi ne da hakan babban abu ne da zai iya sakawa wasu ma su zarge ni kamar yadda Hafiz ma ya kasa yarda da ni shi da yake mijina. Ranar da aka sallamoni daga asibitin tare da Gwaggo na dawo gida, gaba daya tsoron irin tarbon da Baba zai yi min ya gama firgita ni ya saka na fita hayyacina a take, tsoronsa da nake ji a yanzu ya ninka wanda nake ji a lokacin da ban yi aurenba. Ban gane dawowa gidan na zauna kuskure ba ne har sai da gari ya waye, na leka daki na gaishe da Baba ya ki ya amsa min, daman tun da muka shigo be sake min fuska ba. Haka Ya Nabil ma be ce min komai ba, hana ma ta kasa sake min kamar ba ita ba. Within a week na lalace kamar ba ni ba, labarin sakin da aka yi ma ya cika unguwa wasu na tambayar yaushe ma aka yi auren har na dawo gidan, daman sun san ba zan yi zaman aure ba, haka Zainab take fada min yadda ake yawo da ni a unguwa. Ga shi cikin zaman babu dadi domin sun hade min kai, Yaya baya min magana, Hana bata hira da ni iyakacinta idan ta girka abinci ta zuba min ta koma gefe ta zauna, Baba kuma idan ya shigo ba yi masa sannu baya amsa min, idan zai fita ko da safe idan na gaishe shi baya amsa kuma be taba tambayata me ya faru ba!! Haka Mama bata kira ta tambaye ni me ya faru ba, na san kuma ba zata rasa sani ba, domin Ya Nabil yana yawan waya da ita, Hana kuma ta tafi gurinta sau biyu a zuwan da ta yi na karshe take fadawa Yaya jumma'ar ne aka daura mata aure. A tunanina suna min horo ne da wannan saboda a gaba idan na koma kar na sake marmarin dawowa gidan, Sai dai abun da suka kasa fahimta shi ne mace bata sakin kanta, ni kaina na zan iya cewa ga abun da na yi masa ba da har ya saka ya sake ni, saboda suna ganin bana jin magana tun asali ne shiyasa babu wanda zai yarda da ni. Hakan kuma ya saka na ji kamar a gidan yari nake rayuwa saboda kunci da takura, a kowace Sallah sai na roki Allah ya daidaita ni da mijina, sannan na daukarwa kaina alkawari ko da Hafiz sai yanka ni ya ci ko kuma yayi min horo da wuta ba zan taba daga ido na kalleshi ba balle har na yi wani kuskuren da sai saka ya sake sakina. Tsegumin mutane kadai ya ashe ni, wasu har fadar suke wai amanar Zafeer, ba mamaki kuma ta kan iya zaman amanarsa ce ta hana ni zama cikin amincin a gidan Hafiz, domin na cutar da Zafeer na raba kaina da shi da na yi, sanadin Baba wata ila da gaske amanarsa ce Allah kadai ya san halin da ya shiga a sanadin haka. #KhadeejaCandyPAID PAGE 1️⃣2️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Ina ta tsammanin zuwan Hafiz ko Kareem da sunan gyara amman ban ga ko dayansu, hakan kuma ba karamin Mamaki ya ba ni ba, sai na ke ganin kamar daman can Hafiz ba sona yake ba, ya aure ni ne kawai saboda yana son raba ni da wanda ke tsananin kaunata. Sai dai Kareem ya fi ba ni mamaki domin sanadinsa na san Hafiz ko kuma nace Hafiz ya san ni, kuma na kai masa kukana ba sau daya ba amman har yanzu be yi komai ba. Idan na zauna ina tunani sai na ji zuciyata kamar zata fashe, gaba daya na rasa tudun dafawa na rasa ina zan saka kaina na ji sanyi, Mijin da ya dauke ni ya saki ni be waiwayo ba, abokinsa da shi ne sanadin auren be yi wani yunkuri ba, a gidanmu kuma Baba baya min magana saboda yana ganin laifina, Kanwata bata hira da ni, yayana baya kulani na rasa, hakan ya saka na dauki laifin na dorawa kaina. Kullum burina taya zan bullowa lamarin na samu komawa dakin mijina. Da yammancin wata labara na saka hijabina na saka talkamina na fito tsakar gidan. A lokacin Hana ce kadai zaune tana karatun biology, sau daya ta kalleni ta maida kanta bata ce min uffan ba duk kuwa da ta san fita nake da niyar ni. “Hana” Ta juyo ta kalleni ba tare da ta amsa ba. “Abun da kuke min ya dace kenan? Kun maida ni bare a gidan nan?” “Toh ya kike son ayi miki Noor, idan fa ba ki canja hali ba, zaman rayuwar duniya zai miki wuya” “Amman babu wanda ya tambaye waye mai gaskiya me ya faru?” “Baba be son jin uzurinki, saboda ya ci buri a aurenki, na san Baba be kyauta miki ba aura miki wanda baki so, amman be kamata ki ce ba zaki zauna ba, da zarra an daura aure kin tashi daga budurwa Noor, Mama farko bata farinciki da auren amman bayan aurenki nan tana ta jindadin yadda mutane suke yaba gidanki, kuma idan ta duba yadda zaman gidan yake babu dadi sai ta ce kara ma da aka miki auren yanzu ta huta sauran ni, to miye kuma na zuwa ki fito Noor auren da ba a dade da yi ba?” Na share hawayen da suka zubo min. “Ganin kike laifina ne?” “Tohm laifin waye? Mutumen dai yana sonki, ke ce baki son shi, kuma Noor kowa ya san halinki na rashin jin magana sanadin haka kika je kika hadu da wannan mutumen sai kuma yanzu ki dawo kina kame kamen ba zaki zauna ba” “Hannatu ke ma fa mace ce, baki san ya rayuwa zata kasance miki ba, na tabbatar da kin san yadda zafi da bakincikin auren wanda baka so yake da baki fadi haka ba” “Na sani ni mace ce, amman tun yanzu ai ba irin rayuwarki nake ba, kuma bana fatan na yi kalar rayuwarki Noor, ke ce kin son makaranta ke ce jawo ki ce rashin jin magana ke ce saka Mama kuka bakinciki komai dai ke yanzu kuma ana murna an miki aure sai kuma ki kashe auren ki dawo? Yanzu ai sai ki ji idan zaman gidan dadi ne da shi” Bana jin akwai sauran abun da zan fada da zai gamsar da yar'uwata a yanzu, ko kuma ya wanke ni daga mummunan kallon da suke min, gaskiya ta fada da ace ni din kamar ita nake mai jin magana wata kila da yanzu ban samu matsala kamar haka ba. Fita na yi daga gidan ina tafiya jikin ba dadi as well as zuciyata bana iya daga kai na kalli ko'ina har na isa titi, Napep din da ta faka kusa da ni na nufa. Ban tana sanin ina tsananin kaunar Zafeer sai a yau da na yi arba da shi ya fito daga Napep din da nufa zan shiga, ya rame kamar dai he is the only person da na kalla daga fitowa ta gida zuwa nan, shi ma kallona yake kamin ya dauke idonsa ya saka hannunsa aljihu ya dubu daya ya mikawa mai napep din. “Canjin ka kai wannan inda zata je” Wannan karon muna hada ido hawaye suka zubo min. Ya dauke kai ya matsa baya ni kuma na shiga na zauna ina kallonsa har mai napep din ya fara tafiya... “Ina zamu je Hajiya?” A take hankalina ya dawo jikina, kunya da damuwa da bakinciki nadama da kuma dana sani suka rufe ni. Yaushe Zafeer ya dawo garin? Ko dai be tafi ba? Har yanzu yana so na? Ko ya daina? Ya yake kallona? Wata kila ya ji labarin mutuwar aurena amanarshi ta kamani. Ina Son ka Zafeer ina sonka sosai ina son Zafeer Allah ka sani, shi ne abun da nake ta fada a zuciyata, ban hakaro da inda nake ba har sai da Mai napep din ya sake tambayar ina zai kaini. Toh ina zan je kuwa bayan restaurant din Kareem by this time na san Hafiz yana gurinsa, zan fi jindadin tunkararsa a can na bashi hakuri kuma na fada masa ba zan sake aikata kuskure ba, duk kuwa da na san ni din ba ma'asumiya ba ce. Rokonsa a can zai fi min rufin asiri fiye da rokonsa a gidansa kuma a gaban muguwar matarsa wadda ita ce silar faruwar komai. A gaban restaurant din ya sauke ni, ina jin zuciyata kamar ba tawa ba tsananin kunnar da take min, na fito na doshi gate din sai masu gadin suka tare ni. Suna tambayar ina zan tafi, ban yi mamakin jin sabuwar dokarsu ba ta sanin wanda zai fita ko ya shiga, domin aikinsu ne bada tsaro a matsayinsu na masu kula da gate din. Sai dai abun da ya ba ni mamaki shi ne fadar sunana da suka yi, sannan suka tabbatar min da Kareem baya gurin. “Ba gurin Kareem na zo ba, gurin Hafiz na zo” “Shi ma Hafiz din baya nan” “Zan iya shiga na jira?” “Aa gaskiya Oga yace kar abarki ki shiga” Na yi murmushi na juya na kama hanya, yanzu kuma ban san ina zan je ba, ashe abun har ya kai haka? Na zo ace is kar na shiga ciki. Dama na kama na fara tafiya a kafa domin ba ni da kudin abun hawa, idan ma na hau yanzu ban san inda zan je ba. Motar da ke fuskanto ni har ta wuce ni Sai kuma ta dawo ta faka gabana, ban san hawaye nake ba har sai da Kareem ya fito motar ya kalleni ya ce. “Dole ne sai kin fadawa kowa kina cikin damuwa?” Na kai hannu na share hawaye ina kallonsa. “Na zo sun ce kace kar a bar ni na shiga ciki” Ya dan dauke kansa. “Wannan zuwan ba saboda kai ba ne, na zo gurin Hafiz ne, saboda bana son na tafi gurin matarsa kai tsaye, na san a irin wannan lokacin yana gurinka ne, na san na takura maka da yawa Kareem, ba zan sake ba na sani ai na ishe kuwa a yanzu” Ajiyar zuciya na ji ya sauke. “Me Hafiz zai miki?” “Hakuri zan ba shi, zan roki ya maida ni gidansa...” Gambun motar da yake rike da shi ya sake yana kallona kamar mai mamaki. “Noor ba ayi ma namiji haka, shi ya sake ki ai let him come to his senses idan maida ke zai yi sai ya maida ke, amman be kamata ki roke shi ba” “To ya kuke son na yi? Kun raba ni da wanda nake kauna yake so na tsakani da Allah, yanzu kuma abokinka ya sake ni na dawo gida, Baba baya min magana be amsa gaisuwa ta, Hana bata hira da ni, Yaya ko kallona baya yi, a unguwa ana ta yi da ni, Mama tana fushi da ni? So kuke na kashe kaina?” Na karasa maganar ina fasa wani irin ihu kamar wadda ya fita daga hankalinta. Da sauri Kareem ya matso kamar zai rika ni. “Noor... Lafiya” “I'm alright...” Na amsa ina kaucewa daga gabansa na cigaba da tafiya. “Zuwan da kike gurina yana daga cikin abun da yake haddasa fitina tsakaninki da Hafiz, shiyasa na ce kar abarki ki shigo, domin na san zaki sake zuwa ne, a yadda na lura Hafiz yana kishi da hakan, saboda akwai abun da baki sani ba a tsakanina da shi” “Ba zan sake takura muku ba Kareem, ba zan sake zuwa ba” Na fada ba tare da na juyo ba. Sai ya kira ni “Noor...” Na juyo ina wani irin kuka har naman fuskata na rawa. “Hafiz baya garin nan, ya tafi Kaduna gurin wani case tun jiya, amman yau zai dawo. Shim kina son komawa gidansa?” Na daga mishi kai. “Shi kenan, Hafiz zai maida ke na miki alkawari” “Na gode” Na furta daker sannan na juya na cigaba da tafiyar, daga restaurant din zuwa unguwarmu tafiya ce mai nisa amman haka na tako da kafa har gidanmu saboda ba ni da kudin abun hawa kuma na san babu mai ba ni a wannan karon, tufafi ma tun wanda na zo da su daga asibitin ban ni da na canjawa sai dai idan suka yi datti na wanke da ruwa na shaya idan suka bushe na saka, haka nake kamar wata matar gata... Ina shiga gidan, Yaya Nabil ya rufe ni da kuka saboda Baba yayi masa izinin haka, wai na ki zaman aure ina son na fara yawa ina na fito? Gurin uban waye na tafi? Na kasa magana sai kuka nake, duka sosai Yaya yayi min har sai da ya sauya min kamanin fuskata. Baba kuma ya kara min da zagi yana fadin ai ya ji labarin Zafeer ya zo garin nan gurin iyayensa ba mamaki gurinsa na tafi mika hadu. Da rarrafe na shiga dakin na kwamta a kasa a lokacin da ake kiran sallah Magariba a kowane Masallaci, a gurin na kwanta ban iya tashi ba har safe... KAREEM POV. Tsaye yayi a gurin yana ta kallonta tsawon lokacin da ta dauka tana tafiya a kafa har ta karya kwana. Babu abun da yake bata masa rai a rayuwar Noor da Hafiz kamar kasancewa a tsakani, ya zama tsakanin ma'auratan guda biyu, duk ta inda zai motsa kura zai tayar, and the most sadness thing is sanadinsa ne auren ya kullu, ta wani bangaren yana ganin kamar har da rashin so ke wahalar da su, domin ya san yadda zafi da wahalar abun yake, da ace yana sonta da zai iya hakuri da ita a yadda ya same ta ko da kuwa na dan lokaci ne. Shiyasa Noor din ta fi ba shi tausayi domin abokinsa yana da future, yana da matar da yake so take sonsa ya aureta har suka yi zuri'a yanzu. Ita kuma ya rabata da wanda take so kuma yanzu yana wahalar da ita, at her early age lokacin da ya kamata ace tana jindadi. Cikin motar ya koma ya dauki wayarsa sai ya tararda miss calls din Hafiz har biyu, ya dade yana kallon wayar kamar mai tunanin abin yi, har ga Allah be so ya sake yi masa magana akan aurensu ba, domin sakin da Hafiz yayi mata ya bata masa rai, saboda me zai saketa a lokacin da ya same shi ya ba shi shawarar yadda zai zauna da matarsa. Be gama yanke shawarar ba kiran abokinsa ya sake shigowa a karo na uku he pick the call ya kara a kunnensa yayi shiru har sai da Hafiz din ya fara magana cikin farinciki da murna kana jinsa zaka san yana cikin jindadi, daman kuma idan dayansu ya samu wani abun jindadi ko farinciki kamin kowa ya sani sai sun fara labartawa junansu. “I win the case Doctor, we won it...” Kareem yayi murmushi jindadi ya rufe even though dai baya cikin farinciki a yanzu. “Congratulations to us, daman na san zaka yi winning ai, bana da shakkun akanka congrats” “Thank you, ba karamin dadi na ji ba nasarar nan da na samu, domin babban case ne wannan zai kara min martaba sosai zai daga darajar aikina” “Haka ne, ko da yaushe kana nasara Hafiz, kai mutumen mai tsananin jajirce da hikima da wayo tun muna yara, sai dai abun da yake ba ni mamaki shi ne yadda ka gagara fahimtar matanka ka gagara saita gidanka, kuma ka gagara fahimtar wacece ne? Wane irin zama ya dace ka yi da ita, kuma ya kamata ka tafiyar da rayuwarta” “Na fahimci gidana Kareem, na san waye Noor, akwai abun da na fahimta a game ita da zai hanata kuma ni ma ya hana ni jindadin zaman aure da junanmu” “Ka jefa yarinyar a cikin matsala Hafiz, ka rabata da masoyinta mutumen da she can dia for him, ka siye mahaifinta ka aureta yanzu kuma ka sake ta a wace hujja?” Yayi shiru be ce komai ba sai tukin motar yake. “Hafiz, zan roke wannan alfarmar a gareka, zan saka ka aikata saboda ina jin na isa da kai, bayan wannan ba zan sake rokon komai ba, ina son ka maida aurenka da Noor yau... Yarinyar tana wahala ka jefa rayuwarta a masifa, wani abun bakinciki kuma duk saboda ni ne, ka san baka sonta you don't have to married her What kind of wickedness is this? Na taina wayonka Hafiz” “Wait... What....” “Ka mai da aurenka da ita a yau Hafiz...” “Amman kansan bana gari ina hanyar dawowa, na maka alkawari Kareem ina dawowa gidansu zan sauka zan daukota mu tafi gida tare, hakan ya maka..?” “Yayi, thank you my friend” “Ka fi karfin haka, amman ban taba jin ranka ya bace irin haka ba, baka taba bani umarni ko rokona wata alfarma irin wannan ba” Kareem ya sauke ajiyar zuciya shi kanshi ya san he's too harsh for his friend, abun da be saba ba. “ABun ne naka ya daure min kai Hafiz, na rasa gane ma kake nufi fa yarinyar nan, kuma a rasa wanda zai fada maka abun da ka aikata ba daidai ba ne ko Mama ko Baba” “Babu wanda ya san ya sake ta sai Aisha ita kuma na gargadeta kar ta fadawa kowa, Mahaifinta kuma na fada masa zan waiwaye shi, tun daga lokacin ban sake amsa wayarsa ba” “Ka bar abun da ya wuce ya wuce, a fuskanci gaba ita kanta a yanzu na san ta yi sanyi ba zata yi maka laifi ba, sai dai hakan ba zai saka na kasa fada maka ka yi hakuri da Noor ba, ba zan ce ka daina bawa matarka yarda 100% ba, na san maya suna sa wuyar fahimta wuyar sha'ani, but still ka rika bincike kamin ka aiwatar da abu, ka daina compare Noor da AISHA Noor yarinyar kuma bata san komai ba akan aure, Aisha kuma ta waye ta san komai ka tuna ba kai ne first husband dinta ba, kuma Aisha ta yi karatu har degree ba zaka hada ta da Noor da bata ma son zuwa makaranta ba, bawa ta irin wannan wayewar da duniyancin da yan matan yanzu suke da shi, and kishiyace ta koro Aisha daga gidan mijinta na farko, abu ne da ka san shi na san shi, har abada na zata taba son kishiya ba, babu ma macen da zata so kishiya you should think about it Hafiz” “Hmmm...” Kawai Hafiz yace, hango soyayyar Noor da yake a zuciyar abokinsa ne ya hana shi walwala da bude mata nata shafin soyayyar a zuciyarsa, yana rayuwa da matar da ba shi ya kamata ya aureta ba, kuma matar da abokinsa amininsa wanda ya zama dan'uwansa yake sonta, kuma a haka ita kuma a zuciyarta tana son wani dabam ba shi ba. “Sai na dawo...” Ya fada sannan ya kashe wayar. Kareem ya sauke ajiyar zuciya ya yi ma motarsa key ya karasa restaurant. Yana shiga office dinsa Cashier ya shigo suka fara lissafin abubuwa da suka kamata. Be fita ba sai 6pm Kareem ya saka aka kawo masa coffee ya sha saboda ya samu sauki stressed, domin jin yake jikinsa ya mutu gaba daya har wani abu yake ji kamar bachi kamar ba bachi ba. Be bar office din ba sai da aka fara kiran sallah magariba. Yana fitowa sallah kira ya shigo wayarsa, yana ciro wayar ya duba. Number Hafiz ce ba tare da wani dalili ba gabansa ya fadi, babu tsoro ko fargaba amman haka zuciyarsa ta rika bugawa da mugun karfi yana ta kallon wayar tana ringing har ta katse ya kasa amsawa. A karo na biyu da aka sake kiran sai hannunsa da zuciyarsa suka hau rawa. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Ya furta domin be taba jin yanayi irin wannan ba, haka kuma Hafiz be taba kiransa ya gagara amsa wayar ba a yayinda take rike a hannunsa sai yau. Sai da aka sake kira a karo na uku sannan ya iya amsa wayar. “Hello” “Assalamu Alaikum... Barka dai” “Barka ina mai wayar?” Ya tambaya yana jin kirjinsa na masa wani irin nauyi. “Wayar ya samu hatsari a hanyarsa ta shigowa garin Kano, mun samu wayarsa a motarsa sai muka bude da fingerprint dinsa, da muka shiga log calls na sa sai muka samu number ka ne da yayi waya da ita last” “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un... Yana ina?” “Mu sami'an kula da hadarukka ne, yanzu haka muna hanyar asibitin Malam Aminu Kano ne tare da shi” Kareem ya yanke wayar da sauri ya nufi motarsa da gudu ya hau motar ya taka titi kamar wanda baya son rayuwarsa. Kamin su isa asibitin har ya rigasu ya fitowa motarsa ana fitowa da shi daga motar Road safety. Da gudu ya nufi abokinsa dake numfashi daker jini na fita ta cikin kansa. “Hafiz... Hafiz...” Haka ya bi gadonsa da aka dora shi akai aka wuce da shi ICU, Kareem ya dora hannu saman kai kamin ya sauke ya nufi motarsa, wayarsa ya dauko ya kira mahaifin Hafiz, yana dagawa ya ce. “Hafiz din ya rasu ne?” “Aa yanzu suka shigo da shi, Baba kar a fadawa Mama dan Allah” “Tohm ni ma ai sun kira ni, gani nan hanyar asibitin” Ya sauke wayar ya kira mahaifinsa ya fada masa. Yana sauke wayar wani likitan da ya san shi ya fito ya dafa Kareem. “Doctor Kareem, Mutumen yana son magana da kai, ka shiga ka ganshi ka yi abun da ya dace...” Kareem na jin haka gabansa ya tsinke ya fadi, domin shi ma likita ne ya gama fahimtar yaren na su. Cikin rashin kwarin guiwa ya shiga sai ya samu likita uku da Nurses suna kokarin tsayar da jini dake ta zuba amman sun kasa, not because of ba su iya ba, sai dan lokacin tafiya yayi mai ajiya zai karbi abarsa, dabara bata tare damuwa. “Kareem... Allah yayi ba zan samu cika maka burinka ba, ba zan samu dawowa na tafi da Noor ba, ka gyara inda kake ganin na bata, ka san son yarinyar nan Kareem na ga haka a idonta da aikinka, na so ka da farinciki ne shiyasa na so ka aureta, ko yanzu lokaci be kure ba, dan Allah ka auri Noor Kareem ka samawa kanka farinciki, ga Iyeyena nan na bar mana amanarsu, ga Yayana ka ce a kula min da su, na yafewa kowa ka ce kowa ya yafe min, ba zan tashi ba, na san me nake ji na san me nake gani lokacin yayi babu tsayawa...” Magana kawai yake ba dan yana ganin kowa ba domin an yanke ganin, ana saka masa oxygen yana cirewa yana magana daker. Kareem ya rike hannunsa yana kuka. “Yaushe Momy ta tafi, ban gama warkewa daga ciwonta ba zaka tafi ka bar ni Hafiz?” Hafiz ya cire Oxygen din zai yi magana bakinsa ya cika da jini. Sai ya fara kalmar shahada yana tari jinin yana koma masa yana sake fitowa. Mahaifinsa na shigowa wa'adin yana cika rai yayi halinsa Hafiz ya amsa kira... #KhadeejaCandyPAID PAGE 1️⃣2️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Ina ta tsammanin zuwan Hafiz ko Kareem da sunan gyara amman ban ga ko dayansu, hakan kuma ba karamin Mamaki ya ba ni ba, sai na ke ganin kamar daman can Hafiz ba sona yake ba, ya aure ni ne kawai saboda yana son raba ni da wanda ke tsananin kaunata. Sai dai Kareem ya fi ba ni mamaki domin sanadinsa na san Hafiz ko kuma nace Hafiz ya san ni, kuma na kai masa kukana ba sau daya ba amman har yanzu be yi komai ba. Idan na zauna ina tunani sai na ji zuciyata kamar zata fashe, gaba daya na rasa tudun dafawa na rasa ina zan saka kaina na ji sanyi, Mijin da ya dauke ni ya saki ni be waiwayo ba, abokinsa da shi ne sanadin auren be yi wani yunkuri ba, a gidanmu kuma Baba baya min magana saboda yana ganin laifina, Kanwata bata hira da ni, yayana baya kulani na rasa, hakan ya saka na dauki laifin na dorawa kaina. Kullum burina taya zan bullowa lamarin na samu komawa dakin mijina. Da yammancin wata labara na saka hijabina na saka talkamina na fito tsakar gidan. A lokacin Hana ce kadai zaune tana karatun biology, sau daya ta kalleni ta maida kanta bata ce min uffan ba duk kuwa da ta san fita nake da niyar ni. “Hana” Ta juyo ta kalleni ba tare da ta amsa ba. “Abun da kuke min ya dace kenan? Kun maida ni bare a gidan nan?” “Toh ya kike son ayi miki Noor, idan fa ba ki canja hali ba, zaman rayuwar duniya zai miki wuya” “Amman babu wanda ya tambaye waye mai gaskiya me ya faru?” “Baba be son jin uzurinki, saboda ya ci buri a aurenki, na san Baba be kyauta miki ba aura miki wanda baki so, amman be kamata ki ce ba zaki zauna ba, da zarra an daura aure kin tashi daga budurwa Noor, Mama farko bata farinciki da auren amman bayan aurenki nan tana ta jindadin yadda mutane suke yaba gidanki, kuma idan ta duba yadda zaman gidan yake babu dadi sai ta ce kara ma da aka miki auren yanzu ta huta sauran ni, to miye kuma na zuwa ki fito Noor auren da ba a dade da yi ba?” Na share hawayen da suka zubo min. “Ganin kike laifina ne?” “Tohm laifin waye? Mutumen dai yana sonki, ke ce baki son shi, kuma Noor kowa ya san halinki na rashin jin magana sanadin haka kika je kika hadu da wannan mutumen sai kuma yanzu ki dawo kina kame kamen ba zaki zauna ba” “Hannatu ke ma fa mace ce, baki san ya rayuwa zata kasance miki ba, na tabbatar da kin san yadda zafi da bakincikin auren wanda baka so yake da baki fadi haka ba” “Na sani ni mace ce, amman tun yanzu ai ba irin rayuwarki nake ba, kuma bana fatan na yi kalar rayuwarki Noor, ke ce kin son makaranta ke ce jawo ki ce rashin jin magana ke ce saka Mama kuka bakinciki komai dai ke yanzu kuma ana murna an miki aure sai kuma ki kashe auren ki dawo? Yanzu ai sai ki ji idan zaman gidan dadi ne da shi” Bana jin akwai sauran abun da zan fada da zai gamsar da yar'uwata a yanzu, ko kuma ya wanke ni daga mummunan kallon da suke min, gaskiya ta fada da ace ni din kamar ita nake mai jin magana wata kila da yanzu ban samu matsala kamar haka ba. Fita na yi daga gidan ina tafiya jikin ba dadi as well as zuciyata bana iya daga kai na kalli ko'ina har na isa titi, Napep din da ta faka kusa da ni na nufa. Ban tana sanin ina tsananin kaunar Zafeer sai a yau da na yi arba da shi ya fito daga Napep din da nufa zan shiga, ya rame kamar dai he is the only person da na kalla daga fitowa ta gida zuwa nan, shi ma kallona yake kamin ya dauke idonsa ya saka hannunsa aljihu ya dubu daya ya mikawa mai napep din. “Canjin ka kai wannan inda zata je” Wannan karon muna hada ido hawaye suka zubo min. Ya dauke kai ya matsa baya ni kuma na shiga na zauna ina kallonsa har mai napep din ya fara tafiya... “Ina zamu je Hajiya?” A take hankalina ya dawo jikina, kunya da damuwa da bakinciki nadama da kuma dana sani suka rufe ni. Yaushe Zafeer ya dawo garin? Ko dai be tafi ba? Har yanzu yana so na? Ko ya daina? Ya yake kallona? Wata kila ya ji labarin mutuwar aurena amanarshi ta kamani. Ina Son ka Zafeer ina sonka sosai ina son Zafeer Allah ka sani, shi ne abun da nake ta fada a zuciyata, ban hakaro da inda nake ba har sai da Mai napep din ya sake tambayar ina zai kaini. Toh ina zan je kuwa bayan restaurant din Kareem by this time na san Hafiz yana gurinsa, zan fi jindadin tunkararsa a can na bashi hakuri kuma na fada masa ba zan sake aikata kuskure ba, duk kuwa da na san ni din ba ma'asumiya ba ce. Rokonsa a can zai fi min rufin asiri fiye da rokonsa a gidansa kuma a gaban muguwar matarsa wadda ita ce silar faruwar komai. A gaban restaurant din ya sauke ni, ina jin zuciyata kamar ba tawa ba tsananin kunnar da take min, na fito na doshi gate din sai masu gadin suka tare ni. Suna tambayar ina zan tafi, ban yi mamakin jin sabuwar dokarsu ba ta sanin wanda zai fita ko ya shiga, domin aikinsu ne bada tsaro a matsayinsu na masu kula da gate din. Sai dai abun da ya ba ni mamaki shi ne fadar sunana da suka yi, sannan suka tabbatar min da Kareem baya gurin. “Ba gurin Kareem na zo ba, gurin Hafiz na zo” “Shi ma Hafiz din baya nan” “Zan iya shiga na jira?” “Aa gaskiya Oga yace kar abarki ki shiga” Na yi murmushi na juya na kama hanya, yanzu kuma ban san ina zan je ba, ashe abun har ya kai haka? Na zo ace is kar na shiga ciki. Dama na kama na fara tafiya a kafa domin ba ni da kudin abun hawa, idan ma na hau yanzu ban san inda zan je ba. Motar da ke fuskanto ni har ta wuce ni Sai kuma ta dawo ta faka gabana, ban san hawaye nake ba har sai da Kareem ya fito motar ya kalleni ya ce. “Dole ne sai kin fadawa kowa kina cikin damuwa?” Na kai hannu na share hawaye ina kallonsa. “Na zo sun ce kace kar a bar ni na shiga ciki” Ya dan dauke kansa. “Wannan zuwan ba saboda kai ba ne, na zo gurin Hafiz ne, saboda bana son na tafi gurin matarsa kai tsaye, na san a irin wannan lokacin yana gurinka ne, na san na takura maka da yawa Kareem, ba zan sake ba na sani ai na ishe kuwa a yanzu” Ajiyar zuciya na ji ya sauke. “Me Hafiz zai miki?” “Hakuri zan ba shi, zan roki ya maida ni gidansa...” Gambun motar da yake rike da shi ya sake yana kallona kamar mai mamaki. “Noor ba ayi ma namiji haka, shi ya sake ki ai let him come to his senses idan maida ke zai yi sai ya maida ke, amman be kamata ki roke shi ba” “To ya kuke son na yi? Kun raba ni da wanda nake kauna yake so na tsakani da Allah, yanzu kuma abokinka ya sake ni na dawo gida, Baba baya min magana be amsa gaisuwa ta, Hana bata hira da ni, Yaya ko kallona baya yi, a unguwa ana ta yi da ni, Mama tana fushi da ni? So kuke na kashe kaina?” Na karasa maganar ina fasa wani irin ihu kamar wadda ya fita daga hankalinta. Da sauri Kareem ya matso kamar zai rika ni. “Noor... Lafiya” “I'm alright...” Na amsa ina kaucewa daga gabansa na cigaba da tafiya. “Zuwan da kike gurina yana daga cikin abun da yake haddasa fitina tsakaninki da Hafiz, shiyasa na ce kar abarki ki shigo, domin na san zaki sake zuwa ne, a yadda na lura Hafiz yana kishi da hakan, saboda akwai abun da baki sani ba a tsakanina da shi” “Ba zan sake takura muku ba Kareem, ba zan sake zuwa ba” Na fada ba tare da na juyo ba. Sai ya kira ni “Noor...” Na juyo ina wani irin kuka har naman fuskata na rawa. “Hafiz baya garin nan, ya tafi Kaduna gurin wani case tun jiya, amman yau zai dawo. Shim kina son komawa gidansa?” Na daga mishi kai. “Shi kenan, Hafiz zai maida ke na miki alkawari” “Na gode” Na furta daker sannan na juya na cigaba da tafiyar, daga restaurant din zuwa unguwarmu tafiya ce mai nisa amman haka na tako da kafa har gidanmu saboda ba ni da kudin abun hawa kuma na san babu mai ba ni a wannan karon, tufafi ma tun wanda na zo da su daga asibitin ban ni da na canjawa sai dai idan suka yi datti na wanke da ruwa na shaya idan suka bushe na saka, haka nake kamar wata matar gata... Ina shiga gidan, Yaya Nabil ya rufe ni da kuka saboda Baba yayi masa izinin haka, wai na ki zaman aure ina son na fara yawa ina na fito? Gurin uban waye na tafi? Na kasa magana sai kuka nake, duka sosai Yaya yayi min har sai da ya sauya min kamanin fuskata. Baba kuma ya kara min da zagi yana fadin ai ya ji labarin Zafeer ya zo garin nan gurin iyayensa ba mamaki gurinsa na tafi mika hadu. Da rarrafe na shiga dakin na kwamta a kasa a lokacin da ake kiran sallah Magariba a kowane Masallaci, a gurin na kwanta ban iya tashi ba har safe... KAREEM POV. Tsaye yayi a gurin yana ta kallonta tsawon lokacin da ta dauka tana tafiya a kafa har ta karya kwana. Babu abun da yake bata masa rai a rayuwar Noor da Hafiz kamar kasancewa a tsakani, ya zama tsakanin ma'auratan guda biyu, duk ta inda zai motsa kura zai tayar, and the most sadness thing is sanadinsa ne auren ya kullu, ta wani bangaren yana ganin kamar har da rashin so ke wahalar da su, domin ya san yadda zafi da wahalar abun yake, da ace yana sonta da zai iya hakuri da ita a yadda ya same ta ko da kuwa na dan lokaci ne. Shiyasa Noor din ta fi ba shi tausayi domin abokinsa yana da future, yana da matar da yake so take sonsa ya aureta har suka yi zuri'a yanzu. Ita kuma ya rabata da wanda take so kuma yanzu yana wahalar da ita, at her early age lokacin da ya kamata ace tana jindadi. Cikin motar ya koma ya dauki wayarsa sai ya tararda miss calls din Hafiz har biyu, ya dade yana kallon wayar kamar mai tunanin abin yi, har ga Allah be so ya sake yi masa magana akan aurensu ba, domin sakin da Hafiz yayi mata ya bata masa rai, saboda me zai saketa a lokacin da ya same shi ya ba shi shawarar yadda zai zauna da matarsa. Be gama yanke shawarar ba kiran abokinsa ya sake shigowa a karo na uku he pick the call ya kara a kunnensa yayi shiru har sai da Hafiz din ya fara magana cikin farinciki da murna kana jinsa zaka san yana cikin jindadi, daman kuma idan dayansu ya samu wani abun jindadi ko farinciki kamin kowa ya sani sai sun fara labartawa junansu. “I win the case Doctor, we won it...” Kareem yayi murmushi jindadi ya rufe even though dai baya cikin farinciki a yanzu. “Congratulations to us, daman na san zaka yi winning ai, bana da shakkun akanka congrats” “Thank you, ba karamin dadi na ji ba nasarar nan da na samu, domin babban case ne wannan zai kara min martaba sosai zai daga darajar aikina” “Haka ne, ko da yaushe kana nasara Hafiz, kai mutumen mai tsananin jajirce da hikima da wayo tun muna yara, sai dai abun da yake ba ni mamaki shi ne yadda ka gagara fahimtar matanka ka gagara saita gidanka, kuma ka gagara fahimtar wacece ne? Wane irin zama ya dace ka yi da ita, kuma ya kamata ka tafiyar da rayuwarta” “Na fahimci gidana Kareem, na san waye Noor, akwai abun da na fahimta a game ita da zai hanata kuma ni ma ya hana ni jindadin zaman aure da junanmu” “Ka jefa yarinyar a cikin matsala Hafiz, ka rabata da masoyinta mutumen da she can dia for him, ka siye mahaifinta ka aureta yanzu kuma ka sake ta a wace hujja?” Yayi shiru be ce komai ba sai tukin motar yake. “Hafiz, zan roke wannan alfarmar a gareka, zan saka ka aikata saboda ina jin na isa da kai, bayan wannan ba zan sake rokon komai ba, ina son ka maida aurenka da Noor yau... Yarinyar tana wahala ka jefa rayuwarta a masifa, wani abun bakinciki kuma duk saboda ni ne, ka san baka sonta you don't have to married her What kind of wickedness is this? Na taina wayonka Hafiz” “Wait... What....” “Ka mai da aurenka da ita a yau Hafiz...” “Amman kansan bana gari ina hanyar dawowa, na maka alkawari Kareem ina dawowa gidansu zan sauka zan daukota mu tafi gida tare, hakan ya maka..?” “Yayi, thank you my friend” “Ka fi karfin haka, amman ban taba jin ranka ya bace irin haka ba, baka taba bani umarni ko rokona wata alfarma irin wannan ba” Kareem ya sauke ajiyar zuciya shi kanshi ya san he's too harsh for his friend, abun da be saba ba. “ABun ne naka ya daure min kai Hafiz, na rasa gane ma kake nufi fa yarinyar nan, kuma a rasa wanda zai fada maka abun da ka aikata ba daidai ba ne ko Mama ko Baba” “Babu wanda ya san ya sake ta sai Aisha ita kuma na gargadeta kar ta fadawa kowa, Mahaifinta kuma na fada masa zan waiwaye shi, tun daga lokacin ban sake amsa wayarsa ba” “Ka bar abun da ya wuce ya wuce, a fuskanci gaba ita kanta a yanzu na san ta yi sanyi ba zata yi maka laifi ba, sai dai hakan ba zai saka na kasa fada maka ka yi hakuri da Noor ba, ba zan ce ka daina bawa matarka yarda 100% ba, na san maya suna sa wuyar fahimta wuyar sha'ani, but still ka rika bincike kamin ka aiwatar da abu, ka daina compare Noor da AISHA Noor yarinyar kuma bata san komai ba akan aure, Aisha kuma ta waye ta san komai ka tuna ba kai ne first husband dinta ba, kuma Aisha ta yi karatu har degree ba zaka hada ta da Noor da bata ma son zuwa makaranta ba, bawa ta irin wannan wayewar da duniyancin da yan matan yanzu suke da shi, and kishiyace ta koro Aisha daga gidan mijinta na farko, abu ne da ka san shi na san shi, har abada na zata taba son kishiya ba, babu ma macen da zata so kishiya you should think about it Hafiz” “Hmmm...” Kawai Hafiz yace, hango soyayyar Noor da yake a zuciyar abokinsa ne ya hana shi walwala da bude mata nata shafin soyayyar a zuciyarsa, yana rayuwa da matar da ba shi ya kamata ya aureta ba, kuma matar da abokinsa amininsa wanda ya zama dan'uwansa yake sonta, kuma a haka ita kuma a zuciyarta tana son wani dabam ba shi ba. “Sai na dawo...” Ya fada sannan ya kashe wayar. Kareem ya sauke ajiyar zuciya ya yi ma motarsa key ya karasa restaurant. Yana shiga office dinsa Cashier ya shigo suka fara lissafin abubuwa da suka kamata. Be fita ba sai 6pm Kareem ya saka aka kawo masa coffee ya sha saboda ya samu sauki stressed, domin jin yake jikinsa ya mutu gaba daya har wani abu yake ji kamar bachi kamar ba bachi ba. Be bar office din ba sai da aka fara kiran sallah magariba. Yana fitowa sallah kira ya shigo wayarsa, yana ciro wayar ya duba. Number Hafiz ce ba tare da wani dalili ba gabansa ya fadi, babu tsoro ko fargaba amman haka zuciyarsa ta rika bugawa da mugun karfi yana ta kallon wayar tana ringing har ta katse ya kasa amsawa. A karo na biyu da aka sake kiran sai hannunsa da zuciyarsa suka hau rawa. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Ya furta domin be taba jin yanayi irin wannan ba, haka kuma Hafiz be taba kiransa ya gagara amsa wayar ba a yayinda take rike a hannunsa sai yau. Sai da aka sake kira a karo na uku sannan ya iya amsa wayar. “Hello” “Assalamu Alaikum... Barka dai” “Barka ina mai wayar?” Ya tambaya yana jin kirjinsa na masa wani irin nauyi. “Wayar ya samu hatsari a hanyarsa ta shigowa garin Kano, mun samu wayarsa a motarsa sai muka bude da fingerprint dinsa, da muka shiga log calls na sa sai muka samu number ka ne da yayi waya da ita last” “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un... Yana ina?” “Mu sami'an kula da hadarukka ne, yanzu haka muna hanyar asibitin Malam Aminu Kano ne tare da shi” Kareem ya yanke wayar da sauri ya nufi motarsa da gudu ya hau motar ya taka titi kamar wanda baya son rayuwarsa. Kamin su isa asibitin har ya rigasu ya fitowa motarsa ana fitowa da shi daga motar Road safety. Da gudu ya nufi abokinsa dake numfashi daker jini na fita ta cikin kansa. “Hafiz... Hafiz...” Haka ya bi gadonsa da aka dora shi akai aka wuce da shi ICU, Kareem ya dora hannu saman kai kamin ya sauke ya nufi motarsa, wayarsa ya dauko ya kira mahaifin Hafiz, yana dagawa ya ce. “Hafiz din ya rasu ne?” “Aa yanzu suka shigo da shi, Baba kar a fadawa Mama dan Allah” “Tohm ni ma ai sun kira ni, gani nan hanyar asibitin” Ya sauke wayar ya kira mahaifinsa ya fada masa. Yana sauke wayar wani likitan da ya san shi ya fito ya dafa Kareem. “Doctor Kareem, Mutumen yana son magana da kai, ka shiga ka ganshi ka yi abun da ya dace...” Kareem na jin haka gabansa ya tsinke ya fadi, domin shi ma likita ne ya gama fahimtar yaren na su. Cikin rashin kwarin guiwa ya shiga sai ya samu likita uku da Nurses suna kokarin tsayar da jini dake ta zuba amman sun kasa, not because of ba su iya ba, sai dan lokacin tafiya yayi mai ajiya zai karbi abarsa, dabara bata tare damuwa. “Kareem... Allah yayi ba zan samu cika maka burinka ba, ba zan samu dawowa na tafi da Noor ba, ka gyara inda kake ganin na bata, ka san son yarinyar nan Kareem na ga haka a idonta da aikinka, na so ka da farinciki ne shiyasa na so ka aureta, ko yanzu lokaci be kure ba, dan Allah ka auri Noor Kareem ka samawa kanka farinciki, ga Iyeyena nan na bar mana amanarsu, ga Yayana ka ce a kula min da su, na yafewa kowa ka ce kowa ya yafe min, ba zan tashi ba, na san me nake ji na san me nake gani lokacin yayi babu tsayawa...” Magana kawai yake ba dan yana ganin kowa ba domin an yanke ganin, ana saka masa oxygen yana cirewa yana magana daker. Kareem ya rike hannunsa yana kuka. “Yaushe Momy ta tafi, ban gama warkewa daga ciwonta ba zaka tafi ka bar ni Hafiz?” Hafiz ya cire Oxygen din zai yi magana bakinsa ya cika da jini. Sai ya fara kalmar shahada yana tari jinin yana koma masa yana sake fitowa. Mahaifinsa na shigowa wa'adin yana cika rai yayi halinsa Hafiz ya amsa kira... #KhadeejaCandyPAID PAGE 1️⃣3️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Wani abun da Kareem be sake yi ba shi ne hawaye. A gaban idonsa ran abokinsa amininsa abokin shawararsa ya fita. Ya saba ganin mutuwa ya saba sanar da ita ya saba jinta but this one is different mutuwar Hafiz ta yi hitting dinsa in a different way, na farko a lokacin da be yi tsammani ba, kuma a gurin wanda be sakawa ba, mutuwar Momy ta zo masa da sauki domin ta yi ciwo kamin ta rasu, and ko da yaushe tana yawan fadar zata mutu zata mutu tana kan tunatar da su idan sun manta. Amman abokinsa da yake lafiya kalau suka yi waya a hanyarsa ta dawowa har yayi masa alkawarin dawowa da Noor, ta yi hitting dinsa so so so bad. A hanyar da be yi tsammani ba, what a lost, this is a great lost to him ya rasa RAI BIYU within a year... Ya rasa uwa ya rasa babban amininsa. Har kara ma mutuwar Momy ya samu zubar da hawaye yayi kuka a lokacin da ya kebe kansa amman mutuwar Hafiz ta yi hitting dinsa in a way da ta tare hawayensa ta tare zuciyarsa daga kuka tun daga asibitin da mahaifinsa yake kuka har aka dauko gawarsa aka dawo da ita gida gurin iyayensa yan'uwa da matarsa suka rufe gawar da kuka shi kam ko kadan hawaye be kusanci idonsa ba. Kuma ta hana idanuwansa runtsawa a lokacin da ya kwana tare da gawar abokinsa domin yin masa sallama ta karshe.. Da kansa ya wanke abokinsa yayi masa sutura sannan aka jira wayewar gari domin kai shi gidansa na gaskiya. Suna fitowa daga sallah azuba ya shiga cikin gidan ya tambayi mahaifiyar Hafiz ko an sanar da Noor. “Aa ba a fada mata ba, jiya na tambayi Aisha ya ba su zo tare ba sai tace wai tana gidansu ta tafi kusan sati uku bata gidan” “Ya kamata a sanar da ita, hakki ne a fitar mata da shi...” “Aisha tace sakinta yayi, amman be fada mana ba, ko ka sani” “Haka ne, amman tana da hakkin a sanar mata... Mama ki aika a daukota” “Toh ko zaka tafi tare da Raliya sai ku taho da ita, tun da kai ka san gidan” Yayi shiru kamar yace a a sai kuma ya amsa mata da kai ya ce Raliya ta tashi su tafi. Karfe 6am daidai suka faka a kofar gidan. “Shiga ki musu magana” “Tohm...” Ta amsa tana kuka sannan ta bude motar ta fita. NOOR POV. Muna tsaka da tafiya sai na ga sun yi nisa sun bar ni, yana rike da hannun uwargidansa Aisha ita kuma tana rike da hannun yaranta. Gajiya ta saka na zauna a gurin da suka bar ni mai tsananin turbaya da jar kasa, sai dariya nake sun yi nisa sosai kamin Hafiz ya juyo ya kalleni a lokacin ne ya hankara bana tare da su sai ya rugo a ruje ya nufo inda nake yana rike da hannun Aisha ya karaso kusa da ni yana numfashi daker. “Noor taso mu tafi...” Ya miko min hannunsa sai na daga kai na kalleshi sannan na mika masa nawa hannun zai kama kenan kasar da yake tsaye akanta ta bude ta rusga da shi ya fada, sai ya bar mu a gurin ni da Aisha muna kallon ramen da ya fada, ita tana rike da yaransa ni kuma ina daga zaune a gurin domin be kai ga riko ni ba ya fada. Dariyar Aisha ce ta dawo da hankalina zuwa gareta kamin ni ma na fara dariyar sai na mike tsaye. Ban lura ba ashe saman wani tsaye nake tsaye mai tsananin tsawo da saka jiri. Tangal tangal na fara kamar zan fadi sai na ji wani ya rike ni ta dama, yana sakina ya fara tangal tangal wani ya rike ni daga hagu, yana sakina na sake komawa yar gidan jiya, sai kuma na ji an rike ni ta baya, kamin na ji wani dabam kuma ya rumgume ni a kirjinsa, a chest with full of hairy chest har yana shiga min baki. .....Firrrrrrr gigit na farko daga bachin wahala da kuma mafarkin da na tabbatar ba na kwarai ne, domin mafarkin dariya yana nufin bakinciki ga mai yinsa sai dai ta inda ban fahimta me yasa ni da Aisha muke dariyar? Kuma su waye suke rike ni? Waye wanda na kwanta a kirjinsa. Tashi na yi na alwala na rama sallah sannan na gabatar da sallah asuba ina jin fuskata na min yaji saboda dukan da Yaya yayi min ya ji min ciwo a kumatu da gafen ido har ma da saman bakina. Na jingina kadan ina lazimi da hannuna na ji an buga gidanmu, Yaya ne ya bude bana jin me ake cewa amman tabbas na ji yana fadin. “Eh tana nan” Sannan ya kwala min kira na tashi da sauri da kuzari na fita gudun kar na yi laifi. A tsakar gidan na yi arba da kanwar Hafiz, domin Aisha ta gabatar min da su a lokacin da suka zo ina amarya haka ma a burin Walima mun hadu da juna. Hawayen da na gani a idonta ne suke min magana ba bakinta. “Yaya Kareem yana waje ya ce ki zo mu tafi” Na nufi kofar babu talkami a kafata na fice daga gidan zuwa kofar waje. Kareem ya na samu jingine jikin wata bakuwar mota ya rumgume hannayena yana kofar gidanmu. “Hafiz ya rasu...!” Na fada domin a yanzu na gama fahimtar mafarkina. “Ban fada mata ba” Na ji kanwarsa ta fada daga bayana. Juyowa na yi na kalleta. “Na sani, na gani a mafarkina na gani jiya ya saki hannuna ya zo zai kama ni sai wani rame ya bude ya fada da shi, ya saki hannuna da na Aisha, ya tafi ya bar ni ina tangal tangal, wayyo Allah na, na shiga uku wayyo Hafiz...” Na ruka zan kai kasa sai kanwarsa ta rike ni ni da ita muka fashe da kuka mai karfi. “Karfe 8am za ayi masa sallah, you need to be there kamin a tafi da gawarsa” Kareem ya fada ganin kukan na mu ba mai karewa ba ne. Yaya ya leko yana ganin Kareem ya gaishe shi, sai Kareem ya ce. “Ka fadawa Baba Allah yayi ma Hafiz rasuwa jiya da dare, sakamakon hatsarin da yayi a hanyarsa ta dawowa daga Kano” “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Yaya ya fada ya juya ya koma cikin gidan, Kareem kuma ya bude mana mota ni da ita muka shiga baya. Yanzu ta ina zan roki gafararsa ya tafi be fahimce ni ba, ina jiran tsammanin zuwa ko aikowa a dauke ni sai labarin mutuwarsa ya riske ni a yanzu. “Ni ma tawa rayuwar ta kare...!” Wannan kawai na iya furtawa ina kuka bayan haka ban sake fadar komai ba har muka isa gidan. Gidan ya cika tam da mutane amman ba cikar farinciki ba domin kowa kuka yake da jimami. Haka na fito motar babu talkami a kafata kanwarsa ta ja ni ta shiga da ni har gurin da gawar take. Sai ta ja ta tsaya daga bakin kofa ta ni kuma na kwance, yana kwance cikin kagara an masa sutura amman likkafaninsa yana jike da jini. Ban taba arba da gawa ba sai a ranar domin ban taba rasa kowa ba, ban rasa uwa ba ban rasa uba na ban rasa yaya ko kanwa ba. Ban san ya zafin abun yake ba, ban taba zauna a daki daga ni sai gawa ba sai yau. Ashe mijina ne farkon abun da zan fara rasawa a kananan shekaruna... Ban taba sanin idan mutum ya mutu abubuwan da kake masa marar dadi ne suke zuwa su tsaya maka a rai ba sai yau. Yadda yayi ta kokarin kaiwa ga jikina ina hana shi da ihu da kokawa ne ya tsaya min a rai, ya saka ni fasa ihu ya saka ni rawar jiki, me yasa ban bari ya kai ga abun da yake halalinsa ba? Me yasa na biyewa Aisha da tsoro har abubuwa suka zo mana a haka? Ashe zaman ba mai tsawo ba ne ko da na zauna a gidansa ne. Wasu matane ne suka shigo suka fitar da ni, ina wani irin kuka da ban san ina yi ba, sai hakuri suke ba ni suna rarrashina amman ji nake kamar suna cewa bude baki ki yi kuka sosai Noor yau ranar kukanki ce. Ni dai na san bana son Hafiz amman kuma ba kinsa nake ba, amman a ranar na ji tausayinsa kuma na ji tausayin kaina, ban gane haka ba sai da aka fito da gawarsa za a fita da ita domin yi masa sallah. Ban san ya aka yi ba na isa gurin na ratsa cikin maza na rike makara, ina kiran sunansa kamar ance zai iya amsa min. Daker aka banbare hannuna daga jikin makarar su kuka ni kuka ana rike ni aka fita da gawar mijina wanda shi ne duniyata a yanzu. Ban kara raina kaina ba sai da aka kai shi gidansa na gaskiya aka dawo, maza suka shigo cikin gidan domin yi mana gaisuwa, ashe wata kalar azaba ake ji idan aka yi maka gaisuwar wanda ya rasu. Allah ya jikansa yayi masa rahama ya raya abun da ya bari haka kowa yake ta fada. Cikin taron masu yi mana gaisuwa Mama ta kutso ta shigo ta iso inda nake ta zauna sai ta saka hannunta biyu ta rika fuska. “Yi hakuri Noor yi hakuri” Ta fara karanta ayatul kursiyu ta tofa min a kai ta busa ido. Ban sani ba ashe ba daidai nake kallon mutane ba, idanuwan nawa juyewa suka yi ina kallon mutane a baibai. Ta rumgume ni tana kuka, sannan yan'uwanta da na Baba suka shigo suka zauna suna gaisuwar kamar yadda yan'uwan Aisha ma suke cike a gidan, ita ma kuka take tana gurnani ko'ina ana jinta sai hakuri ake bata wasu na addu'ar Allah ya sauke ta lafiya. Ni kuwa a zuciyata ba ni da makiyiya irin Aisha domin ita ce silar duk wata fitina a gidan Hafiz, ashe ma ba dadewa zai yi tare da ni ba, me yasa ta zuge min kunne bata bar ni na yi zaman aure kamar ita ba? Amman laifin ba nata ba ne nawa ne miyasa na dauki zugarta? Why? Har aka yi addu'a uku ban daina ganin laifin kaina ba, kuma ban daina fargabar yadda rayuwa zame min ba bayan tafiyar Hafiz, na san kowa zai dora min laifi ne a gidanmu, kuma na cancanci haka ya kamata ayi min kowane kalar hukunci a yanzu. Na gane ba laifin kowa ba ne nawa, ni ce wawuyar da ban fahimci duniya ba. Wani irin nauyi na ji an dora min ashe haka ko wace mace take ji idan ta rasa abokin rayuwa, ni kenan da ban dade da shi ba kuma ban haihu da shi ba ina ga wandanda suke da yaya kuma suka dade a tare? Wani abun da zan iya cewa tsana ce ko tashin jindadi na ga ganina fuskar iyayen Hafiz bayan sadakan ukun ita ce ta mutuwar auren. Ina da tabbacin a cikinsu babu mai iya bada shaidar abun da ya faru indai ba Aisha ta fada ba, domin sun ce ba su san da sakin ba har sai da ta fada, amman sai na ga nuna min wani kallo, mahaifiyarsa na tambayar me ya hada mu har tana fadan danta mutumen kwarai ne mai mutunci mai rike amana, domin tun da ya auri Aisha ba su taba jin wani abu ba, yana zaune lafiya da matarsa. “Waya sani ma ko bakincikinki ne ya saka shi sakin motar har yaje yayi hatsarin, kin saka na rasa mijina uban Yayana mai so na tsakani da Allah” Na kalli Aisha dake maganar ina hawaye. “Allah ya isa tsakanina dake, ke ce silar da Hafiz ya sake ni, Allah ya isa ban yafe miki ba” “Mijina be san tashin hankali ba sai da ya aureki, daga sunan taimako, Wallahi Hafiz baya sonki shi be taba sonki ba daga ya taimaka ya auroki sai kika zo cikin gidan suna son cin amanarsa” Mahaifinsa ya daka mata tsawa. “Aisha ya isa haka, ko dai minene ya riga ya faru, Allah ya masa rahama, babu amfanin maido baya” “Ai amana bata barin kowa, Allah ya masa rahama, ni dai ina son na tafi da Noor can gidana idan kun yi min izini, yarinya ce ba zata iya wanka ita kadai a gidan ba” “Ai wanka be hau kanta ba domin ya sake ta tun kamin ya rasu, da wanka da gado duk basa kanta” Mahaifinsa ya fada. Sai Aisha ta karba. “Balle ma bata taba yarda da shi ba, kullum addabarsa take da fitina bata taba yarda ya taba ta har ya rasu” Na kalleta ban ce komai ba na dauke kai. Yayan mahaifin Hafiz ne ya ce. “Ko ma dai minene ba mu yanke hukunci ba, sai mun bincike malamai mun ji me ake ciki tukuna, ki tafi da ita din idan mun bincika duk abun da yake nan za mu sanar miki” Yana maganar yana kallon Mama sai ta amsa da tohm. A bisa wannan muka fito daga gidan, wani abun da ban yi tsammani ba shi ne direba ne da mota ya daukemu daga gidansu Iyayen Hafiz zuwa family house din su Mama. Muna shiga kowa sai tausaya min yake suna ta shawarar inda zan zauna a gidan, domin sun ce zaman wanka wai sai da mai kulawa da mace, domin gidan Baba babu mata Hana kuma karamar yarinya ce bata san komai ba. “Ki barta gurin Kawu Garba, matarsa bata da matsala zata kula mata” “Na fa yi magana da Alhaji, shi da kansa ya ce ta zo ta zauna ba wani matsala” Yayanta ya girgiza kai. “Amman Hajara baki yi tunani ba, saure sati daya ki yi masa maganar kawo yarki a gida? Haba dan Allah” “Wallahi Yaya ba ni na yi masa magana ba, tun da aka yi rasuwar na fada masa yace na shirya na zo matarsa ma sau biyu tana zuwa, to kuma jiya da aka yi sadakan uku yake min maganar cewa na maidota a gidan ta zauna tare da ni zata fi sanyi, saman da zaman gidan ubanta domin babu mai kula mata a can din, babu yadda ban yi amman yace na kawota ai kowa ya san lalura ce bata wuce kowa ba, kuma gidan gida ne babba mai yalwa zata iya yin sha'aninta har ya shigo ya fita bata sani ba, domin bangarena dabam bangaren matarsa dabam kuma bangaren nawa ma babba ne sosai” “Aa ni dai ban aminta da hakan ba, kawai dai ya fada ne saboda kawaici, da dai kin hakura ki barta a nan din ta zauna idan ta gama wanka idan ya sake magana sai ta koma amman a yanzu ki barta a nan” Cewar wata yayarta. Sai Mama ta ce “Toh ai na ji suna fadar wai ba zata yi wanka ba, saboda ya sake ta” Yayanta ya kalleni. “Sakinta yayi? Yaushe?” Mama ta fada musu komai sai dai ita ma ba zata iya fadar dalilin sakin ba. Ni kuma na gagara fadar abun da ya gani a jakata har ya zama silar lalacewarki komai. “Ni fa yadda ba lura wannan matar tasa kamar ba ta Allah ba ce, duba yadda yake son kunyata Noor cikin danginsa” “Na lura Wallahi Yaya, ai gata ga su idan wani za su kara aura mata sai mu gani, na san Noor bata jin magana amman a yanzu na lura wannan matar ta fi ta wayo, wata kila da zaman ya dade Allah kadai ya san me zai kasance” Mama ta fada. “Aa laifin duk na wannan yarinyar ne, ba mamaki taje tana masa hauka da nuna masa ita wacan take ba kin san halinta da shirme da shashanci to ya bar miki duniyar kin huta” Cewar Yayanta, haka dai suka ci suka cinye ni dai bana iya cewa komai idona sai ciwo suke saboda kuka da na sha. Daman na san laifin a kaina zai dawo duk juyin da za'ayi ba zan taba wankuwa a idonsu ba. Daga karshe dai aka yanke shawarar bari a gidan Baba domin ya tsaya kai da fata ba zan zauna ko'ina ba sai a gidan, bayan har Kawu Garba ya ce zan zauna a gidansa. A dole na dawo gidan da zama sai wani sabon kunci ya bude min kofa. Hana ta min magana ta kan ja ni da hira Yaya ya kan min magana amman Baba har lokacin fushi yake da ni, yar karamar rayuwar da na yi a gidan Hafiz ta dawo min sabuwa, ina tuna lokacin da ya siya min waya ko kuma yake rarrashina idan kuma na tuna abun da na yi masa na bacin rai sai na ji kamar zan runtse ido na mutu na huta, ina ma ace zai dawo na kyautata masa? Ina ma ace zai dawo ya fahimci ba ni na saka robar nan da magani a jakana ba. But the part da na tuna Aisha tace shi ma haya so na ya kan saka na ji wani iri, be so kuma ya aure ne? Saboda me? Ya san be so ya raba ni da mai so na kuma ya aure ni.... KAREEM POV. Yana zaune a kan tool holding his best friend picture yana kallo, har lokacin baya iya kukan rashin abokinsa zuciyarsa tana nan da nauyinsa pain din ya fi karfin kuka, har gobe he can't believe abokinsa ya tafi ya barshi. “Sun ce mutanen kirki ne suke tafiya da wuri, ka fini kirki har a gurin Allah domin baka aikata abun da nake aikatawa ba, kana kokarin tsare dokokin Allah, kullum burinka na daina abun da nake marar kyau, a lokacin da ka fahimci bana cikin farinciki sai ka fara gina tubalin matso min da shi kusa, maganar mu ta karshe ma umanine kake kokarin cikawa saboda ka faranta min, ba zan taba barin iyalinka su shiga kuncin rashinka ba Hafiz” Yana maganar idonsa suka fara tara hawaye, at the same time Yusura ta turo kofar dakin ta shigo. Kusa da shi ta karaso ta tsaya sai da ta kalli hoton dake hannunsa sannan ta kalli Kareem ta ce “Kyautatawa abokin zama, makoci ko aboki wajibi ne gudun kar ya tafi a dawo nadamar da bata da amfani” Ya aje hoton ya rufe drawer madubin. “A iya sanina Noor bata son Hafiz ko kadan, saboda ya raba ta da wanda take so kuma ya aurenta alhalin shi ma kansa ya san baya sonta kamar dai ke, banbancin mu da su, ba iyaye ne suka cilasta ba, duk wani yunkuri da yake saboda ni ne, daga karshe kuma sai abun ya fada kansa, ashe saboda ya tafi ya bar ni da bakinciki kasa cika masa burinsa ne da ban yi ba...” Ya dago ya kalleta yana murmushi. “Kin san banbancinki da Noor? Ta fi ki wayo ta fi ki imani da yardar da kaddara, ta fi ki tsoron duniya, yarinyar nan bata iya munafurci da pretending ba, tsabar saka shi da ta yi a zuciya na nesan da ta yi na kwana biyu sai da ta yi mafarkin mutuwarsa tun kamin a fada mata ya rasu, a ranar da za a binne Hafiz na ga wani abun da ban yi zato ba gurin yarinyar nan, ta rike karagarsa tana kuka, na tabbatar da ni aka sanar miki na mutu murna zaki yi...” Ta yi murmushi. “Kasan da hakan kuma kake zaune da ni har yanzu? Idan zaka kwatanta Noor da misalta ta da Safeena mana, ka ce ta fi Safeena wayo, amman ba ni ba, ni din na san abun da nake so da wanda bana so. Ko da yake dole ka yaba Noor ai, saboda kana sonta shiyasa ka cilastawa abokinka aurenta, yanzu kuma ya tafi ya barku sai ku cigaba daga inda kuka tsay....” Tana kai aya yana wanke mata fuska da wani zazzafan mari, har sai da ta ja baya “Ka mare ni Kareem? How dare you...!!” “Saki kike so? Tafi na sake ki Yusura” A take ta daina jin zafin marin, farinciki furucinsa ya wanke mata damuwarta. Idan ta tace bata ji tausayin Kareem na mutuwar amininsa ba ta yi karfa haka ma idan tace bata yi farinciki da sakin da Kareem yayi mata a yau ba, ta yi babbar karya. A gurin ta yi sujudar godiya sannan ta mike tsaye ta fice daga dakin. Slowly ya zauna bakin gadonsa be taba tsammanin kiyayyar da Yusura take masa ta kai haka ba. Be yi tunanin akwai kiyayyar da zata kai irin ta Yusura ba a zaman aure, ba zai yana sonta ba, amman baya ganin rabuwa da ita a yanzu mafita ne saboda yaransu. #KhadeejaCandyPAID PAGE 1️⃣3️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Wani abun da Kareem be sake yi ba shi ne hawaye. A gaban idonsa ran abokinsa amininsa abokin shawararsa ya fita. Ya saba ganin mutuwa ya saba sanar da ita ya saba jinta but this one is different mutuwar Hafiz ta yi hitting dinsa in a different way, na farko a lokacin da be yi tsammani ba, kuma a gurin wanda be sakawa ba, mutuwar Momy ta zo masa da sauki domin ta yi ciwo kamin ta rasu, and ko da yaushe tana yawan fadar zata mutu zata mutu tana kan tunatar da su idan sun manta. Amman abokinsa da yake lafiya kalau suka yi waya a hanyarsa ta dawowa har yayi masa alkawarin dawowa da Noor, ta yi hitting dinsa so so so bad. A hanyar da be yi tsammani ba, what a lost, this is a great lost to him ya rasa RAI BIYU within a year... Ya rasa uwa ya rasa babban amininsa. Har kara ma mutuwar Momy ya samu zubar da hawaye yayi kuka a lokacin da ya kebe kansa amman mutuwar Hafiz ta yi hitting dinsa in a way da ta tare hawayensa ta tare zuciyarsa daga kuka tun daga asibitin da mahaifinsa yake kuka har aka dauko gawarsa aka dawo da ita gida gurin iyayensa yan'uwa da matarsa suka rufe gawar da kuka shi kam ko kadan hawaye be kusanci idonsa ba. Kuma ta hana idanuwansa runtsawa a lokacin da ya kwana tare da gawar abokinsa domin yin masa sallama ta karshe.. Da kansa ya wanke abokinsa yayi masa sutura sannan aka jira wayewar gari domin kai shi gidansa na gaskiya. Suna fitowa daga sallah azuba ya shiga cikin gidan ya tambayi mahaifiyar Hafiz ko an sanar da Noor. “Aa ba a fada mata ba, jiya na tambayi Aisha ya ba su zo tare ba sai tace wai tana gidansu ta tafi kusan sati uku bata gidan” “Ya kamata a sanar da ita, hakki ne a fitar mata da shi...” “Aisha tace sakinta yayi, amman be fada mana ba, ko ka sani” “Haka ne, amman tana da hakkin a sanar mata... Mama ki aika a daukota” “Toh ko zaka tafi tare da Raliya sai ku taho da ita, tun da kai ka san gidan” Yayi shiru kamar yace a a sai kuma ya amsa mata da kai ya ce Raliya ta tashi su tafi. Karfe 6am daidai suka faka a kofar gidan. “Shiga ki musu magana” “Tohm...” Ta amsa tana kuka sannan ta bude motar ta fita. NOOR POV. Muna tsaka da tafiya sai na ga sun yi nisa sun bar ni, yana rike da hannun uwargidansa Aisha ita kuma tana rike da hannun yaranta. Gajiya ta saka na zauna a gurin da suka bar ni mai tsananin turbaya da jar kasa, sai dariya nake sun yi nisa sosai kamin Hafiz ya juyo ya kalleni a lokacin ne ya hankara bana tare da su sai ya rugo a ruje ya nufo inda nake yana rike da hannun Aisha ya karaso kusa da ni yana numfashi daker. “Noor taso mu tafi...” Ya miko min hannunsa sai na daga kai na kalleshi sannan na mika masa nawa hannun zai kama kenan kasar da yake tsaye akanta ta bude ta rusga da shi ya fada, sai ya bar mu a gurin ni da Aisha muna kallon ramen da ya fada, ita tana rike da yaransa ni kuma ina daga zaune a gurin domin be kai ga riko ni ba ya fada. Dariyar Aisha ce ta dawo da hankalina zuwa gareta kamin ni ma na fara dariyar sai na mike tsaye. Ban lura ba ashe saman wani tsaye nake tsaye mai tsananin tsawo da saka jiri. Tangal tangal na fara kamar zan fadi sai na ji wani ya rike ni ta dama, yana sakina ya fara tangal tangal wani ya rike ni daga hagu, yana sakina na sake komawa yar gidan jiya, sai kuma na ji an rike ni ta baya, kamin na ji wani dabam kuma ya rumgume ni a kirjinsa, a chest with full of hairy chest har yana shiga min baki. .....Firrrrrrr gigit na farko daga bachin wahala da kuma mafarkin da na tabbatar ba na kwarai ne, domin mafarkin dariya yana nufin bakinciki ga mai yinsa sai dai ta inda ban fahimta me yasa ni da Aisha muke dariyar? Kuma su waye suke rike ni? Waye wanda na kwanta a kirjinsa. Tashi na yi na alwala na rama sallah sannan na gabatar da sallah asuba ina jin fuskata na min yaji saboda dukan da Yaya yayi min ya ji min ciwo a kumatu da gafen ido har ma da saman bakina. Na jingina kadan ina lazimi da hannuna na ji an buga gidanmu, Yaya ne ya bude bana jin me ake cewa amman tabbas na ji yana fadin. “Eh tana nan” Sannan ya kwala min kira na tashi da sauri da kuzari na fita gudun kar na yi laifi. A tsakar gidan na yi arba da kanwar Hafiz, domin Aisha ta gabatar min da su a lokacin da suka zo ina amarya haka ma a burin Walima mun hadu da juna. Hawayen da na gani a idonta ne suke min magana ba bakinta. “Yaya Kareem yana waje ya ce ki zo mu tafi” Na nufi kofar babu talkami a kafata na fice daga gidan zuwa kofar waje. Kareem ya na samu jingine jikin wata bakuwar mota ya rumgume hannayena yana kofar gidanmu. “Hafiz ya rasu...!” Na fada domin a yanzu na gama fahimtar mafarkina. “Ban fada mata ba” Na ji kanwarsa ta fada daga bayana. Juyowa na yi na kalleta. “Na sani, na gani a mafarkina na gani jiya ya saki hannuna ya zo zai kama ni sai wani rame ya bude ya fada da shi, ya saki hannuna da na Aisha, ya tafi ya bar ni ina tangal tangal, wayyo Allah na, na shiga uku wayyo Hafiz...” Na ruka zan kai kasa sai kanwarsa ta rike ni ni da ita muka fashe da kuka mai karfi. “Karfe 8am za ayi masa sallah, you need to be there kamin a tafi da gawarsa” Kareem ya fada ganin kukan na mu ba mai karewa ba ne. Yaya ya leko yana ganin Kareem ya gaishe shi, sai Kareem ya ce. “Ka fadawa Baba Allah yayi ma Hafiz rasuwa jiya da dare, sakamakon hatsarin da yayi a hanyarsa ta dawowa daga Kano” “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Yaya ya fada ya juya ya koma cikin gidan, Kareem kuma ya bude mana mota ni da ita muka shiga baya. Yanzu ta ina zan roki gafararsa ya tafi be fahimce ni ba, ina jiran tsammanin zuwa ko aikowa a dauke ni sai labarin mutuwarsa ya riske ni a yanzu. “Ni ma tawa rayuwar ta kare...!” Wannan kawai na iya furtawa ina kuka bayan haka ban sake fadar komai ba har muka isa gidan. Gidan ya cika tam da mutane amman ba cikar farinciki ba domin kowa kuka yake da jimami. Haka na fito motar babu talkami a kafata kanwarsa ta ja ni ta shiga da ni har gurin da gawar take. Sai ta ja ta tsaya daga bakin kofa ta ni kuma na kwance, yana kwance cikin kagara an masa sutura amman likkafaninsa yana jike da jini. Ban taba arba da gawa ba sai a ranar domin ban taba rasa kowa ba, ban rasa uwa ba ban rasa uba na ban rasa yaya ko kanwa ba. Ban san ya zafin abun yake ba, ban taba zauna a daki daga ni sai gawa ba sai yau. Ashe mijina ne farkon abun da zan fara rasawa a kananan shekaruna... Ban taba sanin idan mutum ya mutu abubuwan da kake masa marar dadi ne suke zuwa su tsaya maka a rai ba sai yau. Yadda yayi ta kokarin kaiwa ga jikina ina hana shi da ihu da kokawa ne ya tsaya min a rai, ya saka ni fasa ihu ya saka ni rawar jiki, me yasa ban bari ya kai ga abun da yake halalinsa ba? Me yasa na biyewa Aisha da tsoro har abubuwa suka zo mana a haka? Ashe zaman ba mai tsawo ba ne ko da na zauna a gidansa ne. Wasu matane ne suka shigo suka fitar da ni, ina wani irin kuka da ban san ina yi ba, sai hakuri suke ba ni suna rarrashina amman ji nake kamar suna cewa bude baki ki yi kuka sosai Noor yau ranar kukanki ce. Ni dai na san bana son Hafiz amman kuma ba kinsa nake ba, amman a ranar na ji tausayinsa kuma na ji tausayin kaina, ban gane haka ba sai da aka fito da gawarsa za a fita da ita domin yi masa sallah. Ban san ya aka yi ba na isa gurin na ratsa cikin maza na rike makara, ina kiran sunansa kamar ance zai iya amsa min. Daker aka banbare hannuna daga jikin makarar su kuka ni kuka ana rike ni aka fita da gawar mijina wanda shi ne duniyata a yanzu. Ban kara raina kaina ba sai da aka kai shi gidansa na gaskiya aka dawo, maza suka shigo cikin gidan domin yi mana gaisuwa, ashe wata kalar azaba ake ji idan aka yi maka gaisuwar wanda ya rasu. Allah ya jikansa yayi masa rahama ya raya abun da ya bari haka kowa yake ta fada. Cikin taron masu yi mana gaisuwa Mama ta kutso ta shigo ta iso inda nake ta zauna sai ta saka hannunta biyu ta rika fuska. “Yi hakuri Noor yi hakuri” Ta fara karanta ayatul kursiyu ta tofa min a kai ta busa ido. Ban sani ba ashe ba daidai nake kallon mutane ba, idanuwan nawa juyewa suka yi ina kallon mutane a baibai. Ta rumgume ni tana kuka, sannan yan'uwanta da na Baba suka shigo suka zauna suna gaisuwar kamar yadda yan'uwan Aisha ma suke cike a gidan, ita ma kuka take tana gurnani ko'ina ana jinta sai hakuri ake bata wasu na addu'ar Allah ya sauke ta lafiya. Ni kuwa a zuciyata ba ni da makiyiya irin Aisha domin ita ce silar duk wata fitina a gidan Hafiz, ashe ma ba dadewa zai yi tare da ni ba, me yasa ta zuge min kunne bata bar ni na yi zaman aure kamar ita ba? Amman laifin ba nata ba ne nawa ne miyasa na dauki zugarta? Why? Har aka yi addu'a uku ban daina ganin laifin kaina ba, kuma ban daina fargabar yadda rayuwa zame min ba bayan tafiyar Hafiz, na san kowa zai dora min laifi ne a gidanmu, kuma na cancanci haka ya kamata ayi min kowane kalar hukunci a yanzu. Na gane ba laifin kowa ba ne nawa, ni ce wawuyar da ban fahimci duniya ba. Wani irin nauyi na ji an dora min ashe haka ko wace mace take ji idan ta rasa abokin rayuwa, ni kenan da ban dade da shi ba kuma ban haihu da shi ba ina ga wandanda suke da yaya kuma suka dade a tare? Wani abun da zan iya cewa tsana ce ko tashin jindadi na ga ganina fuskar iyayen Hafiz bayan sadakan ukun ita ce ta mutuwar auren. Ina da tabbacin a cikinsu babu mai iya bada shaidar abun da ya faru indai ba Aisha ta fada ba, domin sun ce ba su san da sakin ba har sai da ta fada, amman sai na ga nuna min wani kallo, mahaifiyarsa na tambayar me ya hada mu har tana fadan danta mutumen kwarai ne mai mutunci mai rike amana, domin tun da ya auri Aisha ba su taba jin wani abu ba, yana zaune lafiya da matarsa. “Waya sani ma ko bakincikinki ne ya saka shi sakin motar har yaje yayi hatsarin, kin saka na rasa mijina uban Yayana mai so na tsakani da Allah” Na kalli Aisha dake maganar ina hawaye. “Allah ya isa tsakanina dake, ke ce silar da Hafiz ya sake ni, Allah ya isa ban yafe miki ba” “Mijina be san tashin hankali ba sai da ya aureki, daga sunan taimako, Wallahi Hafiz baya sonki shi be taba sonki ba daga ya taimaka ya auroki sai kika zo cikin gidan suna son cin amanarsa” Mahaifinsa ya daka mata tsawa. “Aisha ya isa haka, ko dai minene ya riga ya faru, Allah ya masa rahama, babu amfanin maido baya” “Ai amana bata barin kowa, Allah ya masa rahama, ni dai ina son na tafi da Noor can gidana idan kun yi min izini, yarinya ce ba zata iya wanka ita kadai a gidan ba” “Ai wanka be hau kanta ba domin ya sake ta tun kamin ya rasu, da wanka da gado duk basa kanta” Mahaifinsa ya fada. Sai Aisha ta karba. “Balle ma bata taba yarda da shi ba, kullum addabarsa take da fitina bata taba yarda ya taba ta har ya rasu” Na kalleta ban ce komai ba na dauke kai. Yayan mahaifin Hafiz ne ya ce. “Ko ma dai minene ba mu yanke hukunci ba, sai mun bincike malamai mun ji me ake ciki tukuna, ki tafi da ita din idan mun bincika duk abun da yake nan za mu sanar miki” Yana maganar yana kallon Mama sai ta amsa da tohm. A bisa wannan muka fito daga gidan, wani abun da ban yi tsammani ba shi ne direba ne da mota ya daukemu daga gidansu Iyayen Hafiz zuwa family house din su Mama. Muna shiga kowa sai tausaya min yake suna ta shawarar inda zan zauna a gidan, domin sun ce zaman wanka wai sai da mai kulawa da mace, domin gidan Baba babu mata Hana kuma karamar yarinya ce bata san komai ba. “Ki barta gurin Kawu Garba, matarsa bata da matsala zata kula mata” “Na fa yi magana da Alhaji, shi da kansa ya ce ta zo ta zauna ba wani matsala” Yayanta ya girgiza kai. “Amman Hajara baki yi tunani ba, saure sati daya ki yi masa maganar kawo yarki a gida? Haba dan Allah” “Wallahi Yaya ba ni na yi masa magana ba, tun da aka yi rasuwar na fada masa yace na shirya na zo matarsa ma sau biyu tana zuwa, to kuma jiya da aka yi sadakan uku yake min maganar cewa na maidota a gidan ta zauna tare da ni zata fi sanyi, saman da zaman gidan ubanta domin babu mai kula mata a can din, babu yadda ban yi amman yace na kawota ai kowa ya san lalura ce bata wuce kowa ba, kuma gidan gida ne babba mai yalwa zata iya yin sha'aninta har ya shigo ya fita bata sani ba, domin bangarena dabam bangaren matarsa dabam kuma bangaren nawa ma babba ne sosai” “Aa ni dai ban aminta da hakan ba, kawai dai ya fada ne saboda kawaici, da dai kin hakura ki barta a nan din ta zauna idan ta gama wanka idan ya sake magana sai ta koma amman a yanzu ki barta a nan” Cewar wata yayarta. Sai Mama ta ce “Toh ai na ji suna fadar wai ba zata yi wanka ba, saboda ya sake ta” Yayanta ya kalleni. “Sakinta yayi? Yaushe?” Mama ta fada musu komai sai dai ita ma ba zata iya fadar dalilin sakin ba. Ni kuma na gagara fadar abun da ya gani a jakata har ya zama silar lalacewarki komai. “Ni fa yadda ba lura wannan matar tasa kamar ba ta Allah ba ce, duba yadda yake son kunyata Noor cikin danginsa” “Na lura Wallahi Yaya, ai gata ga su idan wani za su kara aura mata sai mu gani, na san Noor bata jin magana amman a yanzu na lura wannan matar ta fi ta wayo, wata kila da zaman ya dade Allah kadai ya san me zai kasance” Mama ta fada. “Aa laifin duk na wannan yarinyar ne, ba mamaki taje tana masa hauka da nuna masa ita wacan take ba kin san halinta da shirme da shashanci to ya bar miki duniyar kin huta” Cewar Yayanta, haka dai suka ci suka cinye ni dai bana iya cewa komai idona sai ciwo suke saboda kuka da na sha. Daman na san laifin a kaina zai dawo duk juyin da za'ayi ba zan taba wankuwa a idonsu ba. Daga karshe dai aka yanke shawarar bari a gidan Baba domin ya tsaya kai da fata ba zan zauna ko'ina ba sai a gidan, bayan har Kawu Garba ya ce zan zauna a gidansa. A dole na dawo gidan da zama sai wani sabon kunci ya bude min kofa. Hana ta min magana ta kan ja ni da hira Yaya ya kan min magana amman Baba har lokacin fushi yake da ni, yar karamar rayuwar da na yi a gidan Hafiz ta dawo min sabuwa, ina tuna lokacin da ya siya min waya ko kuma yake rarrashina idan kuma na tuna abun da na yi masa na bacin rai sai na ji kamar zan runtse ido na mutu na huta, ina ma ace zai dawo na kyautata masa? Ina ma ace zai dawo ya fahimci ba ni na saka robar nan da magani a jakana ba. But the part da na tuna Aisha tace shi ma haya so na ya kan saka na ji wani iri, be so kuma ya aure ne? Saboda me? Ya san be so ya raba ni da mai so na kuma ya aure ni.... KAREEM POV. Yana zaune a kan tool holding his best friend picture yana kallo, har lokacin baya iya kukan rashin abokinsa zuciyarsa tana nan da nauyinsa pain din ya fi karfin kuka, har gobe he can't believe abokinsa ya tafi ya barshi. “Sun ce mutanen kirki ne suke tafiya da wuri, ka fini kirki har a gurin Allah domin baka aikata abun da nake aikatawa ba, kana kokarin tsare dokokin Allah, kullum burinka na daina abun da nake marar kyau, a lokacin da ka fahimci bana cikin farinciki sai ka fara gina tubalin matso min da shi kusa, maganar mu ta karshe ma umanine kake kokarin cikawa saboda ka faranta min, ba zan taba barin iyalinka su shiga kuncin rashinka ba Hafiz” Yana maganar idonsa suka fara tara hawaye, at the same time Yusura ta turo kofar dakin ta shigo. Kusa da shi ta karaso ta tsaya sai da ta kalli hoton dake hannunsa sannan ta kalli Kareem ta ce “Kyautatawa abokin zama, makoci ko aboki wajibi ne gudun kar ya tafi a dawo nadamar da bata da amfani” Ya aje hoton ya rufe drawer madubin. “A iya sanina Noor bata son Hafiz ko kadan, saboda ya raba ta da wanda take so kuma ya aurenta alhalin shi ma kansa ya san baya sonta kamar dai ke, banbancin mu da su, ba iyaye ne suka cilasta ba, duk wani yunkuri da yake saboda ni ne, daga karshe kuma sai abun ya fada kansa, ashe saboda ya tafi ya bar ni da bakinciki kasa cika masa burinsa ne da ban yi ba...” Ya dago ya kalleta yana murmushi. “Kin san banbancinki da Noor? Ta fi ki wayo ta fi ki imani da yardar da kaddara, ta fi ki tsoron duniya, yarinyar nan bata iya munafurci da pretending ba, tsabar saka shi da ta yi a zuciya na nesan da ta yi na kwana biyu sai da ta yi mafarkin mutuwarsa tun kamin a fada mata ya rasu, a ranar da za a binne Hafiz na ga wani abun da ban yi zato ba gurin yarinyar nan, ta rike karagarsa tana kuka, na tabbatar da ni aka sanar miki na mutu murna zaki yi...” Ta yi murmushi. “Kasan da hakan kuma kake zaune da ni har yanzu? Idan zaka kwatanta Noor da misalta ta da Safeena mana, ka ce ta fi Safeena wayo, amman ba ni ba, ni din na san abun da nake so da wanda bana so. Ko da yake dole ka yaba Noor ai, saboda kana sonta shiyasa ka cilastawa abokinka aurenta, yanzu kuma ya tafi ya barku sai ku cigaba daga inda kuka tsay....” Tana kai aya yana wanke mata fuska da wani zazzafan mari, har sai da ta ja baya “Ka mare ni Kareem? How dare you...!!” “Saki kike so? Tafi na sake ki Yusura” A take ta daina jin zafin marin, farinciki furucinsa ya wanke mata damuwarta. Idan ta tace bata ji tausayin Kareem na mutuwar amininsa ba ta yi karfa haka ma idan tace bata yi farinciki da sakin da Kareem yayi mata a yau ba, ta yi babbar karya. A gurin ta yi sujudar godiya sannan ta mike tsaye ta fice daga dakin. Slowly ya zauna bakin gadonsa be taba tsammanin kiyayyar da Yusura take masa ta kai haka ba. Be yi tunanin akwai kiyayyar da zata kai irin ta Yusura ba a zaman aure, ba zai yana sonta ba, amman baya ganin rabuwa da ita a yanzu mafita ne saboda yaransu. #KhadeejaCandyPAID PAGE 1️⃣3️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Wani abun da Kareem be sake yi ba shi ne hawaye. A gaban idonsa ran abokinsa amininsa abokin shawararsa ya fita. Ya saba ganin mutuwa ya saba sanar da ita ya saba jinta but this one is different mutuwar Hafiz ta yi hitting dinsa in a different way, na farko a lokacin da be yi tsammani ba, kuma a gurin wanda be sakawa ba, mutuwar Momy ta zo masa da sauki domin ta yi ciwo kamin ta rasu, and ko da yaushe tana yawan fadar zata mutu zata mutu tana kan tunatar da su idan sun manta. Amman abokinsa da yake lafiya kalau suka yi waya a hanyarsa ta dawowa har yayi masa alkawarin dawowa da Noor, ta yi hitting dinsa so so so bad. A hanyar da be yi tsammani ba, what a lost, this is a great lost to him ya rasa RAI BIYU within a year... Ya rasa uwa ya rasa babban amininsa. Har kara ma mutuwar Momy ya samu zubar da hawaye yayi kuka a lokacin da ya kebe kansa amman mutuwar Hafiz ta yi hitting dinsa in a way da ta tare hawayensa ta tare zuciyarsa daga kuka tun daga asibitin da mahaifinsa yake kuka har aka dauko gawarsa aka dawo da ita gida gurin iyayensa yan'uwa da matarsa suka rufe gawar da kuka shi kam ko kadan hawaye be kusanci idonsa ba. Kuma ta hana idanuwansa runtsawa a lokacin da ya kwana tare da gawar abokinsa domin yin masa sallama ta karshe.. Da kansa ya wanke abokinsa yayi masa sutura sannan aka jira wayewar gari domin kai shi gidansa na gaskiya. Suna fitowa daga sallah azuba ya shiga cikin gidan ya tambayi mahaifiyar Hafiz ko an sanar da Noor. “Aa ba a fada mata ba, jiya na tambayi Aisha ya ba su zo tare ba sai tace wai tana gidansu ta tafi kusan sati uku bata gidan” “Ya kamata a sanar da ita, hakki ne a fitar mata da shi...” “Aisha tace sakinta yayi, amman be fada mana ba, ko ka sani” “Haka ne, amman tana da hakkin a sanar mata... Mama ki aika a daukota” “Toh ko zaka tafi tare da Raliya sai ku taho da ita, tun da kai ka san gidan” Yayi shiru kamar yace a a sai kuma ya amsa mata da kai ya ce Raliya ta tashi su tafi. Karfe 6am daidai suka faka a kofar gidan. “Shiga ki musu magana” “Tohm...” Ta amsa tana kuka sannan ta bude motar ta fita. NOOR POV. Muna tsaka da tafiya sai na ga sun yi nisa sun bar ni, yana rike da hannun uwargidansa Aisha ita kuma tana rike da hannun yaranta. Gajiya ta saka na zauna a gurin da suka bar ni mai tsananin turbaya da jar kasa, sai dariya nake sun yi nisa sosai kamin Hafiz ya juyo ya kalleni a lokacin ne ya hankara bana tare da su sai ya rugo a ruje ya nufo inda nake yana rike da hannun Aisha ya karaso kusa da ni yana numfashi daker. “Noor taso mu tafi...” Ya miko min hannunsa sai na daga kai na kalleshi sannan na mika masa nawa hannun zai kama kenan kasar da yake tsaye akanta ta bude ta rusga da shi ya fada, sai ya bar mu a gurin ni da Aisha muna kallon ramen da ya fada, ita tana rike da yaransa ni kuma ina daga zaune a gurin domin be kai ga riko ni ba ya fada. Dariyar Aisha ce ta dawo da hankalina zuwa gareta kamin ni ma na fara dariyar sai na mike tsaye. Ban lura ba ashe saman wani tsaye nake tsaye mai tsananin tsawo da saka jiri. Tangal tangal na fara kamar zan fadi sai na ji wani ya rike ni ta dama, yana sakina ya fara tangal tangal wani ya rike ni daga hagu, yana sakina na sake komawa yar gidan jiya, sai kuma na ji an rike ni ta baya, kamin na ji wani dabam kuma ya rumgume ni a kirjinsa, a chest with full of hairy chest har yana shiga min baki. .....Firrrrrrr gigit na farko daga bachin wahala da kuma mafarkin da na tabbatar ba na kwarai ne, domin mafarkin dariya yana nufin bakinciki ga mai yinsa sai dai ta inda ban fahimta me yasa ni da Aisha muke dariyar? Kuma su waye suke rike ni? Waye wanda na kwanta a kirjinsa. Tashi na yi na alwala na rama sallah sannan na gabatar da sallah asuba ina jin fuskata na min yaji saboda dukan da Yaya yayi min ya ji min ciwo a kumatu da gafen ido har ma da saman bakina. Na jingina kadan ina lazimi da hannuna na ji an buga gidanmu, Yaya ne ya bude bana jin me ake cewa amman tabbas na ji yana fadin. “Eh tana nan” Sannan ya kwala min kira na tashi da sauri da kuzari na fita gudun kar na yi laifi. A tsakar gidan na yi arba da kanwar Hafiz, domin Aisha ta gabatar min da su a lokacin da suka zo ina amarya haka ma a burin Walima mun hadu da juna. Hawayen da na gani a idonta ne suke min magana ba bakinta. “Yaya Kareem yana waje ya ce ki zo mu tafi” Na nufi kofar babu talkami a kafata na fice daga gidan zuwa kofar waje. Kareem ya na samu jingine jikin wata bakuwar mota ya rumgume hannayena yana kofar gidanmu. “Hafiz ya rasu...!” Na fada domin a yanzu na gama fahimtar mafarkina. “Ban fada mata ba” Na ji kanwarsa ta fada daga bayana. Juyowa na yi na kalleta. “Na sani, na gani a mafarkina na gani jiya ya saki hannuna ya zo zai kama ni sai wani rame ya bude ya fada da shi, ya saki hannuna da na Aisha, ya tafi ya bar ni ina tangal tangal, wayyo Allah na, na shiga uku wayyo Hafiz...” Na ruka zan kai kasa sai kanwarsa ta rike ni ni da ita muka fashe da kuka mai karfi. “Karfe 8am za ayi masa sallah, you need to be there kamin a tafi da gawarsa” Kareem ya fada ganin kukan na mu ba mai karewa ba ne. Yaya ya leko yana ganin Kareem ya gaishe shi, sai Kareem ya ce. “Ka fadawa Baba Allah yayi ma Hafiz rasuwa jiya da dare, sakamakon hatsarin da yayi a hanyarsa ta dawowa daga Kano” “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Yaya ya fada ya juya ya koma cikin gidan, Kareem kuma ya bude mana mota ni da ita muka shiga baya. Yanzu ta ina zan roki gafararsa ya tafi be fahimce ni ba, ina jiran tsammanin zuwa ko aikowa a dauke ni sai labarin mutuwarsa ya riske ni a yanzu. “Ni ma tawa rayuwar ta kare...!” Wannan kawai na iya furtawa ina kuka bayan haka ban sake fadar komai ba har muka isa gidan. Gidan ya cika tam da mutane amman ba cikar farinciki ba domin kowa kuka yake da jimami. Haka na fito motar babu talkami a kafata kanwarsa ta ja ni ta shiga da ni har gurin da gawar take. Sai ta ja ta tsaya daga bakin kofa ta ni kuma na kwance, yana kwance cikin kagara an masa sutura amman likkafaninsa yana jike da jini. Ban taba arba da gawa ba sai a ranar domin ban taba rasa kowa ba, ban rasa uwa ba ban rasa uba na ban rasa yaya ko kanwa ba. Ban san ya zafin abun yake ba, ban taba zauna a daki daga ni sai gawa ba sai yau. Ashe mijina ne farkon abun da zan fara rasawa a kananan shekaruna... Ban taba sanin idan mutum ya mutu abubuwan da kake masa marar dadi ne suke zuwa su tsaya maka a rai ba sai yau. Yadda yayi ta kokarin kaiwa ga jikina ina hana shi da ihu da kokawa ne ya tsaya min a rai, ya saka ni fasa ihu ya saka ni rawar jiki, me yasa ban bari ya kai ga abun da yake halalinsa ba? Me yasa na biyewa Aisha da tsoro har abubuwa suka zo mana a haka? Ashe zaman ba mai tsawo ba ne ko da na zauna a gidansa ne. Wasu matane ne suka shigo suka fitar da ni, ina wani irin kuka da ban san ina yi ba, sai hakuri suke ba ni suna rarrashina amman ji nake kamar suna cewa bude baki ki yi kuka sosai Noor yau ranar kukanki ce. Ni dai na san bana son Hafiz amman kuma ba kinsa nake ba, amman a ranar na ji tausayinsa kuma na ji tausayin kaina, ban gane haka ba sai da aka fito da gawarsa za a fita da ita domin yi masa sallah. Ban san ya aka yi ba na isa gurin na ratsa cikin maza na rike makara, ina kiran sunansa kamar ance zai iya amsa min. Daker aka banbare hannuna daga jikin makarar su kuka ni kuka ana rike ni aka fita da gawar mijina wanda shi ne duniyata a yanzu. Ban kara raina kaina ba sai da aka kai shi gidansa na gaskiya aka dawo, maza suka shigo cikin gidan domin yi mana gaisuwa, ashe wata kalar azaba ake ji idan aka yi maka gaisuwar wanda ya rasu. Allah ya jikansa yayi masa rahama ya raya abun da ya bari haka kowa yake ta fada. Cikin taron masu yi mana gaisuwa Mama ta kutso ta shigo ta iso inda nake ta zauna sai ta saka hannunta biyu ta rika fuska. “Yi hakuri Noor yi hakuri” Ta fara karanta ayatul kursiyu ta tofa min a kai ta busa ido. Ban sani ba ashe ba daidai nake kallon mutane ba, idanuwan nawa juyewa suka yi ina kallon mutane a baibai. Ta rumgume ni tana kuka, sannan yan'uwanta da na Baba suka shigo suka zauna suna gaisuwar kamar yadda yan'uwan Aisha ma suke cike a gidan, ita ma kuka take tana gurnani ko'ina ana jinta sai hakuri ake bata wasu na addu'ar Allah ya sauke ta lafiya. Ni kuwa a zuciyata ba ni da makiyiya irin Aisha domin ita ce silar duk wata fitina a gidan Hafiz, ashe ma ba dadewa zai yi tare da ni ba, me yasa ta zuge min kunne bata bar ni na yi zaman aure kamar ita ba? Amman laifin ba nata ba ne nawa ne miyasa na dauki zugarta? Why? Har aka yi addu'a uku ban daina ganin laifin kaina ba, kuma ban daina fargabar yadda rayuwa zame min ba bayan tafiyar Hafiz, na san kowa zai dora min laifi ne a gidanmu, kuma na cancanci haka ya kamata ayi min kowane kalar hukunci a yanzu. Na gane ba laifin kowa ba ne nawa, ni ce wawuyar da ban fahimci duniya ba. Wani irin nauyi na ji an dora min ashe haka ko wace mace take ji idan ta rasa abokin rayuwa, ni kenan da ban dade da shi ba kuma ban haihu da shi ba ina ga wandanda suke da yaya kuma suka dade a tare? Wani abun da zan iya cewa tsana ce ko tashin jindadi na ga ganina fuskar iyayen Hafiz bayan sadakan ukun ita ce ta mutuwar auren. Ina da tabbacin a cikinsu babu mai iya bada shaidar abun da ya faru indai ba Aisha ta fada ba, domin sun ce ba su san da sakin ba har sai da ta fada, amman sai na ga nuna min wani kallo, mahaifiyarsa na tambayar me ya hada mu har tana fadan danta mutumen kwarai ne mai mutunci mai rike amana, domin tun da ya auri Aisha ba su taba jin wani abu ba, yana zaune lafiya da matarsa. “Waya sani ma ko bakincikinki ne ya saka shi sakin motar har yaje yayi hatsarin, kin saka na rasa mijina uban Yayana mai so na tsakani da Allah” Na kalli Aisha dake maganar ina hawaye. “Allah ya isa tsakanina dake, ke ce silar da Hafiz ya sake ni, Allah ya isa ban yafe miki ba” “Mijina be san tashin hankali ba sai da ya aureki, daga sunan taimako, Wallahi Hafiz baya sonki shi be taba sonki ba daga ya taimaka ya auroki sai kika zo cikin gidan suna son cin amanarsa” Mahaifinsa ya daka mata tsawa. “Aisha ya isa haka, ko dai minene ya riga ya faru, Allah ya masa rahama, babu amfanin maido baya” “Ai amana bata barin kowa, Allah ya masa rahama, ni dai ina son na tafi da Noor can gidana idan kun yi min izini, yarinya ce ba zata iya wanka ita kadai a gidan ba” “Ai wanka be hau kanta ba domin ya sake ta tun kamin ya rasu, da wanka da gado duk basa kanta” Mahaifinsa ya fada. Sai Aisha ta karba. “Balle ma bata taba yarda da shi ba, kullum addabarsa take da fitina bata taba yarda ya taba ta har ya rasu” Na kalleta ban ce komai ba na dauke kai. Yayan mahaifin Hafiz ne ya ce. “Ko ma dai minene ba mu yanke hukunci ba, sai mun bincike malamai mun ji me ake ciki tukuna, ki tafi da ita din idan mun bincika duk abun da yake nan za mu sanar miki” Yana maganar yana kallon Mama sai ta amsa da tohm. A bisa wannan muka fito daga gidan, wani abun da ban yi tsammani ba shi ne direba ne da mota ya daukemu daga gidansu Iyayen Hafiz zuwa family house din su Mama. Muna shiga kowa sai tausaya min yake suna ta shawarar inda zan zauna a gidan, domin sun ce zaman wanka wai sai da mai kulawa da mace, domin gidan Baba babu mata Hana kuma karamar yarinya ce bata san komai ba. “Ki barta gurin Kawu Garba, matarsa bata da matsala zata kula mata” “Na fa yi magana da Alhaji, shi da kansa ya ce ta zo ta zauna ba wani matsala” Yayanta ya girgiza kai. “Amman Hajara baki yi tunani ba, saure sati daya ki yi masa maganar kawo yarki a gida? Haba dan Allah” “Wallahi Yaya ba ni na yi masa magana ba, tun da aka yi rasuwar na fada masa yace na shirya na zo matarsa ma sau biyu tana zuwa, to kuma jiya da aka yi sadakan uku yake min maganar cewa na maidota a gidan ta zauna tare da ni zata fi sanyi, saman da zaman gidan ubanta domin babu mai kula mata a can din, babu yadda ban yi amman yace na kawota ai kowa ya san lalura ce bata wuce kowa ba, kuma gidan gida ne babba mai yalwa zata iya yin sha'aninta har ya shigo ya fita bata sani ba, domin bangarena dabam bangaren matarsa dabam kuma bangaren nawa ma babba ne sosai” “Aa ni dai ban aminta da hakan ba, kawai dai ya fada ne saboda kawaici, da dai kin hakura ki barta a nan din ta zauna idan ta gama wanka idan ya sake magana sai ta koma amman a yanzu ki barta a nan” Cewar wata yayarta. Sai Mama ta ce “Toh ai na ji suna fadar wai ba zata yi wanka ba, saboda ya sake ta” Yayanta ya kalleni. “Sakinta yayi? Yaushe?” Mama ta fada musu komai sai dai ita ma ba zata iya fadar dalilin sakin ba. Ni kuma na gagara fadar abun da ya gani a jakata har ya zama silar lalacewarki komai. “Ni fa yadda ba lura wannan matar tasa kamar ba ta Allah ba ce, duba yadda yake son kunyata Noor cikin danginsa” “Na lura Wallahi Yaya, ai gata ga su idan wani za su kara aura mata sai mu gani, na san Noor bata jin magana amman a yanzu na lura wannan matar ta fi ta wayo, wata kila da zaman ya dade Allah kadai ya san me zai kasance” Mama ta fada. “Aa laifin duk na wannan yarinyar ne, ba mamaki taje tana masa hauka da nuna masa ita wacan take ba kin san halinta da shirme da shashanci to ya bar miki duniyar kin huta” Cewar Yayanta, haka dai suka ci suka cinye ni dai bana iya cewa komai idona sai ciwo suke saboda kuka da na sha. Daman na san laifin a kaina zai dawo duk juyin da za'ayi ba zan taba wankuwa a idonsu ba. Daga karshe dai aka yanke shawarar bari a gidan Baba domin ya tsaya kai da fata ba zan zauna ko'ina ba sai a gidan, bayan har Kawu Garba ya ce zan zauna a gidansa. A dole na dawo gidan da zama sai wani sabon kunci ya bude min kofa. Hana ta min magana ta kan ja ni da hira Yaya ya kan min magana amman Baba har lokacin fushi yake da ni, yar karamar rayuwar da na yi a gidan Hafiz ta dawo min sabuwa, ina tuna lokacin da ya siya min waya ko kuma yake rarrashina idan kuma na tuna abun da na yi masa na bacin rai sai na ji kamar zan runtse ido na mutu na huta, ina ma ace zai dawo na kyautata masa? Ina ma ace zai dawo ya fahimci ba ni na saka robar nan da magani a jakana ba. But the part da na tuna Aisha tace shi ma haya so na ya kan saka na ji wani iri, be so kuma ya aure ne? Saboda me? Ya san be so ya raba ni da mai so na kuma ya aure ni.... KAREEM POV. Yana zaune a kan tool holding his best friend picture yana kallo, har lokacin baya iya kukan rashin abokinsa zuciyarsa tana nan da nauyinsa pain din ya fi karfin kuka, har gobe he can't believe abokinsa ya tafi ya barshi. “Sun ce mutanen kirki ne suke tafiya da wuri, ka fini kirki har a gurin Allah domin baka aikata abun da nake aikatawa ba, kana kokarin tsare dokokin Allah, kullum burinka na daina abun da nake marar kyau, a lokacin da ka fahimci bana cikin farinciki sai ka fara gina tubalin matso min da shi kusa, maganar mu ta karshe ma umanine kake kokarin cikawa saboda ka faranta min, ba zan taba barin iyalinka su shiga kuncin rashinka ba Hafiz” Yana maganar idonsa suka fara tara hawaye, at the same time Yusura ta turo kofar dakin ta shigo. Kusa da shi ta karaso ta tsaya sai da ta kalli hoton dake hannunsa sannan ta kalli Kareem ta ce “Kyautatawa abokin zama, makoci ko aboki wajibi ne gudun kar ya tafi a dawo nadamar da bata da amfani” Ya aje hoton ya rufe drawer madubin. “A iya sanina Noor bata son Hafiz ko kadan, saboda ya raba ta da wanda take so kuma ya aurenta alhalin shi ma kansa ya san baya sonta kamar dai ke, banbancin mu da su, ba iyaye ne suka cilasta ba, duk wani yunkuri da yake saboda ni ne, daga karshe kuma sai abun ya fada kansa, ashe saboda ya tafi ya bar ni da bakinciki kasa cika masa burinsa ne da ban yi ba...” Ya dago ya kalleta yana murmushi. “Kin san banbancinki da Noor? Ta fi ki wayo ta fi ki imani da yardar da kaddara, ta fi ki tsoron duniya, yarinyar nan bata iya munafurci da pretending ba, tsabar saka shi da ta yi a zuciya na nesan da ta yi na kwana biyu sai da ta yi mafarkin mutuwarsa tun kamin a fada mata ya rasu, a ranar da za a binne Hafiz na ga wani abun da ban yi zato ba gurin yarinyar nan, ta rike karagarsa tana kuka, na tabbatar da ni aka sanar miki na mutu murna zaki yi...” Ta yi murmushi. “Kasan da hakan kuma kake zaune da ni har yanzu? Idan zaka kwatanta Noor da misalta ta da Safeena mana, ka ce ta fi Safeena wayo, amman ba ni ba, ni din na san abun da nake so da wanda bana so. Ko da yake dole ka yaba Noor ai, saboda kana sonta shiyasa ka cilastawa abokinka aurenta, yanzu kuma ya tafi ya barku sai ku cigaba daga inda kuka tsay....” Tana kai aya yana wanke mata fuska da wani zazzafan mari, har sai da ta ja baya “Ka mare ni Kareem? How dare you...!!” “Saki kike so? Tafi na sake ki Yusura” A take ta daina jin zafin marin, farinciki furucinsa ya wanke mata damuwarta. Idan ta tace bata ji tausayin Kareem na mutuwar amininsa ba ta yi karfa haka ma idan tace bata yi farinciki da sakin da Kareem yayi mata a yau ba, ta yi babbar karya. A gurin ta yi sujudar godiya sannan ta mike tsaye ta fice daga dakin. Slowly ya zauna bakin gadonsa be taba tsammanin kiyayyar da Yusura take masa ta kai haka ba. Be yi tunanin akwai kiyayyar da zata kai irin ta Yusura ba a zaman aure, ba zai yana sonta ba, amman baya ganin rabuwa da ita a yanzu mafita ne saboda yaransu. #KhadeejaCandyBaba yana kallona ne kamar ni na kashe Hafiz saboda, Hafiz ya tafi be samu kyautatawa Baba kamar gyara masa gida ko kuma yi masa wata babbar kyauta da yake tsammani ba tun a bayan aurena. Ni ma ban fahimci hakan ba sai a ranar da Hafiz ya cika sati daya da barin duniya, Mama ta kira waya tana kara kwantar min da hankali, bayan mun gama wayar ne Baba ya rufe ni da fada wai na ci amanarsa wata kila da na kyautata masa da yanzu Allah kadai ya san yadda rayuwa zata zame mana. “Daman sai da zuciyata ta raya min ba zaman lafiya kike da yaron nan ba, saboda juya min baya da yayi ko lokacin da gobarar nan ta tashi be zo yayi min jaje ba, be ba ni komai ba, ashe ma ba zai dade duniyar ba, kina ta shuka masa rashin mutunci, in ba shi ba taya za su ce wai ba za ki masa wanka ba? Ta ina aka taba haka so suke su hana miki gadonsa kenan” Ni dai bance komai ba, gaba daya duniyar bata min dadi, ni kaina ina dorawa kaina nauyin da ba zai gogu ba saboda hana mijina hakkinsa da na yi, ya tafi da abun a ransa kuma na daukarwa kaina zunubi. “Wallahi zan iya kararsu akan haka, domin babu hujjar da tace ba za a baki gado ba, na bincike limin yace kina da hakkin wanka domin an riga da an daura muku aure, kuma sakin da yayi miki ai ba ki cika idda ba” Sai a lokacin na kalleshi cikin wani irin rauni da damuwa na ce. “Baba dan Allah ko da sun ce ba za su ba ni hakkin wanka ba, dan girman Allah dan Isar Annabi, Baba kar kace zaka yi kara ko fada ko kuma daukar wani mataki, dan Allah ka kyale su, idan ma ina da hakki Allah ya sani zai saka min” “Toh haka za a zuba musu ido su ci su cinye hakkinki Noor? Idan aka karba ai ko wani abun a rage da shi, dubi yadda gidan nan yake fa, ko gyara aka yi ba a rage ba? Allah kadai ya san abun da bawan Allah nan ya bari” “Ko ma dai miye bari Baba mai karewa ne, rayuwar ma ta kare balle kuma abun da rayuwarta ta aje, ni dai da zaka yarda da magana ta Baba da ka yi hakuri ka kyale komai dan Allah” “Ai daman ke sakarya ce baki san komai ba, sai shashanshanci, ba dan kin nuna masa rashin tarbiya da rashin hankali ba yaushe zai sake ki? Allah ya wadarranki Noor, duk yadda nake ganin kamar zaki natsu ko ki yi hankali ba zaki taba yi ba, duk yadda bake ganin kamar sanadinki wata kila zan warke sai kin kunyartar da ni, ke dai har abada va yar arziki ba ce” Ya rufe da fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba. Ni dai kam na san ban yi dacen abubuwa da yawa ba a rayuwa ciki har da uba. Domin ko a labari ban taba jin uba makamancin nawa ba, mai tsananin kwadayi da son abun duniya. Na sani sarai idan na kara wata maganar zai iya rufe ni da duka, a dole na yi shiru na ina ta sauraren masifarsa har yayi ya gama ya fice daga gidan. Haka na gagara tashi a gurin har Hana ta dawo daga makaranta ta same ni zaune a kofar dakin, ni ba kuka nake ba damuwa karara a fuskata, tunanin yadda rayuwa zata zame min nake, hankali ko tunanin da suke ganin kamar ba ni da shi ina da shi, ni na san ina da shi, idan ma babu a da to yanzu yana tare da ni. Rayuwar gidance nake jin kamar ba zata min dadin zama ba, gashi kuma ba ni da wani gurin rabawa da zan zauna na ji sanyi. Yunkurawa na yi na tashi na nufi gurin da kayan wanke wankemu suke na wanke komai tass Hana kuma ta dora girki ta girka mana shimkafa da miya, duk da kasancewa white rice and stew are my favorite amman ban iya cin wani abun kirki ba, daman abinci ya daina burge ni. Kamar wani zanenen al'amari a daren da muka yi haka da Baba sai ga kanen margayi ya zo gidanmu, ban san ya aka yi ya gane gidan ba, kusan ni dai zan iya cewa ban taba ganinsa ba, idan ma na ganshi ba zan iya shaidar fuskarsa ba, domin ban jima a gidan ba balle na san duka yan'uwansa balle kuma mazan da be gabatar min da su ba. A zauren gidanmu ya shigo bayan yayi sallama Hana ta yi masa izinin shigowa. Dogon hijab ne a jikina har kasa kaina kuma a kasa na kasa kallonsa ganin nake kowa kallona yake a wani muhalli da Aisha ta saka ni a idonsu. Bayan mun gaisa ya gyara tsayuwarsa ya ce. “Ya Hakuri Noor?” “Alhamdullahi” “Haka Allah ya so sai hakuri, shi kuma Allah yayi masa rahama” “Ameen” Na amsa ina jin idanuwa suna cika da kwalla. “Na san babu dadi, musamman ma ke da kike farkon shiga gidansa ba ki jima ba mutuwa ta yi muku gaggawa, amman duk da haka ki yi hakuri yana cikin jarabawa ne” “Haka ne, na gode” “Na san ba ki san ni sosai ba, ni kane ne a gurin Margayi uwa daya uba daya, ni ne kanensa na biyu, makasodin zuwa na a nan shi ne... Abubuwa marasa dadi sun shiga kuma za su biyo baya na sani, amman dan Allah ina son ku kawar da kanku musamman ma ke, ki yi hakuri da abubuwan da zaki ji ko ki gani” Na yi shiru ina ta sauraren bayaninsa da ban fahimci inda ya dosa ba. “Na ji wasu abubuwan ne da ba su min dadi a gidanmu, na iya yadda zan iya na taushe abun amman ya gagara saboda haihuwarmu aka yi ba mu muka haife su ba, dole sai hakuri, amman na san ke zan iya neman alfarma a gurinki kuma na roke ki duk kuwa da ba ki san ni ba, amman ina rokon alfarmar dan Allah karki ce zaki yi jayayya da iyayen margayi akan gadonki, ke ba da kike da shi ba balle ace saboda da gaba, kina gama wanka na san In Shaa Allahu zaki yi aurenki, bana son na ji wata matsala ta taso daga gurinki, ni dai ina kyautata miki zato sosai” “Ni ba zan iya jayaya akan abun da rai ya tara kuma ya tafi ya bari ba, wanda ya tara abun ma ina yake? Toh me zai saka ni yin jayayya? Idan ma ina da hakki abun da za su ba ni ba zai taka kara ya karya ba, ba shi ne gabana ba, kuma na maka alkawari ba zaka taba jin wani abu makamancin wannan daga bangarena ba” Ya sauke ajiyar zuciya yana kallona. “Na yi farinciki da jin haka, na jidadi sosai Allah ya saka miki da alheri, ya baki wanda zai maye miki gurbin Ya Hafiz har ma ya fi shi” Na yi shiru ban iya amsawa da Ameen ba. Daga haka yayi min sallama ya tafi, ni kuma na dawo cikin gidan ina ta mamaki mi ya ji danginsa ana fada har dauko kafafuwansa ya zo ya tari nawa fadan, ni kan idan gado ne ko nawa ne ba zai daga min hankali ba balle ya saka ni yin magana ko daukar wata dokar tsorona duk na Baba ne. Ban fadawa Baba wani ya zo ba, sai dai na lura hakan be yanke komai daga hanzarinsa na niyar saka iyayen Hafiz a kotu ba, idan har ba su ba da hakkina na wanka ba, na fahinci hakan ne ta dalilin wayar da na ji yana yi da yayansa wai ya bincika ko'ina ance ina da gado, dan haka ba zai saka musu ido su cinye min hakkin ba. Ban ce komai ba daman kuma ban isa na ce ya rufe da fada ba mamaki ma ya kara min duka. Zaman gidan sam baya min dadi kamar ina zaune a kaya haka nake ji. Ba ka kamar lokacin da sabuwar matar da Baba ya aura ta tare a gidan. Gaba daya sai gidan ya kara fice min a rai, domin na lura ta shigo da wani salo na hana mu walwala ni da Hana da kuma Yaya, gara ma yaya ba a gidan yake wuni ba, sai dare yake dawowa ni da Hana ne muke ganin rayuwa a gidan. Babu kuma wanda ya isa yayi magana domin mun san halin Baba ba zai taba yarda da mu ba. Umma bata wuce wata biyu ba a gidan ta cigaba da sana'o'inta da take, daman na ji Hana na fadar wai ance tana siyar da kunun waken soya kuma tana wara tana kosai, domin ba yar garin Kano ba ce asalinta yar riɓa ce dake can kusa da zuru ta birnin kebbi amman take zaune a nan Kano gurin Yayarta bayan rasuwar mijinta na farko, tana sana'a har Allah ya kawo mata Baba ya aureta a yanzu. Bata taba haihuwa ba a wacan auren nata kamar yadda take labarta masa wani lokaci ni da hana, ba wata babbar mace ce be domin Mama ta yi kanwa da ita ta biyu, sai dai tana da irin jikin nan sosai da zata iya daukar Mama da irinta uku ta goya ta gudu, domin ni da Mama jikinmu daya, ita ba kiba ni ma babu kibar, ba mamaki ma kibar ce ta burge Baba ya aurota. Wani sabon salo da ta kirkira shi ne na dorawa Hana tallar awarar a titi tana siyar mata kullum zata bata 500 naira, ita kuma tana yin kunun waken soyar a gida, ana shigowa ana siya sai dai ba sosai kamar yadda take fada mana ba. Dole ce ta saka Hana yarda tana soya mana awara a waje ba dan tana so ba, domin ko a lokacin da Mama take gidan kuma muke cikin tsananin shan wahala bata taba gwada dora mana talla ba, amman ita wannan da ba uwarmu ba ta fara dora ma Hana talla daga zuwanta. Ko da yake ba laifinta babne laifin Baba domin shi ya bata dama Hana kuma bata isa tace ba zata yi ba, duk kuwa da kasancewar bata so ko kadan. Domin fita tallar ya kashe mata tafiya makarantar yamma, ya zama boko kawai take iya tafiya da safe. Ni kuma aka bar ni da wahalar aikin gidan, shara wanke wanke da hura wuta tun ban iya ba har na iya, girkin ne kawai bata bari na yi domin na gwada girkanwa ta ji be yi mata yadda take ba. Idan zata hada kunun wanken soyan ni nake wanke goruna ni nake mata komai har tacewa, awara kuma ni zan gyara wake da dare da safe taje ta kanta ta kai nika, idan ta dafa a tare zamu natse ni zan yanka idan aka soya be wuce a ba ni da hansin ba ko saba'in. Wani sabon shafin wahalar rayuwa Umma ta bude mana a idan, ni da Hana saboda sana'ar da take wai ai ba ita zata fita ta yi ba a dole hana zata soya mana wara a waje ni kuma na yi aikin cikin gida. Ta inda nake samun sauki shi ne takaba da nake bana fita, saboda haka duk wani aiki na fita ita zata fita ta yi, da safe kuma Yaya sai ya cika gidan da ruwa sannan yake fita. Ta inda gurin da ta samu banbancin da Mama a zamanta gidan ita kam Baba yana bata abinci da cefane mai kyau, ba kamar Mama ba da wani lokacin zai ce be da shi ko kuma ya bada abinci ya hana cefane ko ma ya hana gaba daya. Wata kila saboda ita din tana da dan da sauran kurciya ba kamar Mama ba, wata kila kuma dokin amarci ne yake Allah masani. Idan kuma aka yi girki ba a ba mu wani abun arziki Allah ma ya sa yanzu damuwa bata barina na ci na koshi kamar da, wani lokacin har ragewa nake na bawa Hana a da kam na fi kowa cin abinci a gidan, ranar da Hana ta tafi family house din Mama ta fada musu halin da ake ciki na dora mata talla, washe gari Kawu Garba ya samu Baba yana nuna masa hakan be dace ba, sai Baba yace kar wanda ya sake saka masa baki akan lamarin yaransa shi ya ga damar su yi, kuma babu mai ciyar masa da yara sai su. A nan yake fadar ai tun kamin auren ya fada mata yaransa za su rika mata wani abun saboda ta fada masa ita fa tana sana'a kuma aure ba zai hana ta yi ba, shi kuma ba zai iya ganin matarsa da aure ta fita waje ta yi sana'ar wara ba, domin haka yarsa zata maye masa gurbi. Ni kam gaba daya na zama kamar ba ni ba duk abun da ake bana iya cewa komai sai ido, wani kalar canji ne ya same ni irin wanda ban yi zato ba. KAREEM POV. Da kansa ya shiryawa yaransa abun karyawa ya dauko lunch box dinsu ya raka su har gurin School bus suka shiga sannan ya juyo ya dawo, dakinsa ya shiga yayi wanka ya shirya ya fito ya shiga motarsa. Family house dinsu ya wuce domin fara gaisawa da iyayensa kamin ya wuce aiki kasancewar yau Monday. Wani abun da ya sabawa kansa da shi ne, na kin kallon mahaifiyarsa a duk lokacin da ya shiga gidan. Kai tsaye ya wuce bangaren Hajiya Hassana wadda take step mom dinsa. Karyawa ya same ta tana yi tare da Khadija da Aaryam da sauran yaransa Aneesa da Kamla. Kanensa duk suka gaishe shi ya amsa, Yusura dake zaune gefe daya ta mike tsaye ta shige dakin Hajiya Hassana sai a lokacin ma Kareem ya lura da ita. Khadija ta kwashi kayan abincin ta bi bayan Yusura Kamla da Anessa ma haka, sai ya rage daga Step Mom dinsa sai kanensa Aaryam. “Zaka ci abincin a zuba maka?” Hajiya ta tambaya. “Aa” “Baka cin abinci yanzu, tun da Momynka bata nan, shigowa nan ma sai monday Monday kake yi ka duba mu, idan Momynka bata nan ni da mahaifinka ai muna nan kuma Kanenka suna nan be kamata kana haka ba” A hankali ya sauke ajiyar zuciya. “Hajiya Bana jindadin shigowa ne yana yawan tuna min da Momy kuma ina jin babu dadi” “Tohm ya za'ayi haka tsarin Allah yake, kai kanka mutuwa zaka yi balle kuma wasu, sai hakuri rayuwa ta gaji haka, ni kaina yanzu gidan ba dadi yake min ba Wallahi, amman a haka nake daurewa saboda Khadija da Aaryam da kuma Aneesah, dole na yi walwala idan ba haka ba dukanmu sai mu taru mu takura mu yi ta bakinciki da kuka” Yayi shiru be ce komai ba. Hajiya ta dauki tissue ta goge hannunta. “Likita..” Ta kira shi sai ya kalleta daman haka take kiransa tun Momy na gidan. “Ni fa ba zan boye maka ba, ban gane manufar abun da ka yi ba, kuma ban gane inda kuka dosa ba” “Na miye ba Hajiya?” “Kai da Yusura mana, ta dawo gida kawai tace mana ka sake ta, saki daya biyu ko uku ba mu sani ba, Daddy ka ma fushi yake da kai shiyasa be maka maganar ba har yau, Khadija da Aaryam ma gashi a zaune kullum haushinka suke ji saboda haka” Kareem ya juya ya kalli Aaryam kyakkyawan saurayi mai jini a jika, sai yayi murmushi. “Saboda Yusura?” “Eh mana, Daddynka cewa yayi ba zai maka magana ba, kuma kar wanda yayi maka a saka maka ido kawai, ita kuma ta so barin gidan ni na hana, saboda na san idan Momynku tana raye Yusura bata da gurin zama sai gidan nan, a nan ta girma nan ta saba yanzu kuma dan Momy bata nan babu wanda zan bari ya dauketa ko kuma ita ta tafi ta bar mu, sai idan na mutu, kai ma dan kana ganin Momy bata nan ya saka kake son ka wulakanta amanar da ta baka, to ka sani Yusura ta fika gata a gidan nan, kuma matukar ina raye ni ce gatanta ba kuma zata wulakanta ba” Kareem yayi gutun murmushi ya girgiza kai, kana ya sake juyawa ya kalli Saurayin Kanensa ya ce. “Fushi kuke ta yi da ni akan abun da Baku san komai a kai ba” Aaryam ya ce. “Haba Big Bro ko dai minene ai be kamata ace ta kai ga haka ba, kai fa Namiji ne, kuma ga yara tsakaninku, kawai dai ban maka magana ba ne saboda Daddy yace kowa ya saka maka ido, kuma ina kasa da kai be kamata na tsuma baki a irin wannan ba sai idan ka bukata” “Gaskiya ne” Kareem ya fada tare da aje numfashi sannan ya mike tsaye ya nufi bangaren mahaifinsu, sai a yanzu ya fahimci dalilin da ya saka har yau da suke wata biyu da sati biyu da rabuwa Daddy be taba kiransa ya tambaye shi miye ya faru ba, kuma be taba yi masa maganar ba a duk shigowar da yake gaishe shi a gidan. A natse ya shiga bangaren kamar yadda ya saba sai bayan da ya zauna sannan ya gaishe da Daddy dake sanye da gilashi yana duba newspaper. “Lafiya Kalau, Kareem ya gidan ya yaran?” “Lafiya kalau Daddy” “Maa Shaa Allah, yau Monday ko akwai aiki” “Haka ne Daddy” “Allah ya taimaka ya bada nasara” “Ameen” Kareem ya mike tsaye har ya fara tafiya sai kuma ya dawo ya zauna yana kallon Daddy. Daddyn ma ya kalleshi “Allah yasa lafiya, akwai wata matsala ne?” Kareem ya hade wani abun da ya tsaya masa a makoshi sannan ya ce. “Daddy, ban ji kace komai akan dawowa Yusura gidan nan ba” Daddy ya aje newspaper dake hannunsa. “Oh wai Yusura, Mijinta ne ya sake ta kasan kuma bata da wani gidan da ya wuce nan, bata da gata a duniyar nan sai mu, zamanta a nan ya takura maka ne? So kake a koreta?” Kareem yayi murmushi jin yadda Daddy yake fadar mijinta ne ya saketa kamar be san Kareem din ne mijinta ba. “Aa Daddy ai ban isa na ce a koreta ba” “Good kara dai da kasan haka” Ya sake yin murmushi, a yanzu ne ya kara tabbatar Daddy fushi yake da shi. “Kawai dai na yi zaton ko zaka bincike abun da ya faru ne” “Abun da ya faru, tsohuwar budurwarka tana zuwan nemanka, amaryar abokinka tana zuwan nemanka ta yi magana sai ka mareta ka ce ka saketa” Dif Kareem ya dauke wuta kamin ya kalli Daddy ya ce. “Haka ta fada maka?” “Ba gaskiya ba ne Daddy, Safeena ta zo gaisuwar Momy ne, kuma na gargade kar ta sake zuwa domin babu wata alaka tsakanina da ita, Noor kuma tana zuwa ne saboda tsabanin da suke samu da Hafiz a lokacin” “Zan yarda da wannan, domin ban san ka da wani aiki na assha ba, shi ma wannan saboda Hassana ta matsa ne ya saka ta fadi wannan dalilin, amman bayan haka bata fada mana komai ba, ni kuma na auna abun a ma'aunin kishi ne, sai dai kai kuma ka yi kuskure na aikata saki a take” Kareem yayi shiru kamar ba zai ce komai ba. Daddy ya cigaba. “Shiyasa na yi shiru na zuba maka ido na gani shin kana da hankali kansan ya kamata ko baka sani ba”Kareem ya sauke numfashi mai nauyi. “Daddy, akwai abubuwan da ni da ita muka boye ba mu bar kowa ya sani ba, ban san ya zaka fahimta ba gaskiya ce mai matukar nauyi da daure kai, Daddy ni da Yusura ba mu taba son junanmu ba, ban taba jin ina sonta ba ita ma bata taba jin tana so na, wannan sakin ma ta dade tana bukatar na yi mata shi, saboda da nisanta da ni” Daddy yayi murmushi mai sauki ya cire gilashin idonsa. “Kareem karka maida karamin yaro mana, baka sonta bata sonka aka yi muku aure kuka zauna lafiya har kuka haihu ba a taba jin kanku ba sai yanzu da Mahaifiyarka bata raye zaka ce wai baka sonta? Wannan ba hujja ba ce” Cikin tsananin damuwa Kareem ya ce. “Wallahi Daddy bana son Yusura ita ma bata so na, kawai dai mun amsawa Momy ne kuma mun zauna saboda ita, ni da ita ba za mu iya bijirewa umarninta ba” “Okay yanzu da bata raye mu ne abokan wasarka? Kai da ita? Ni ba zan ma yarda ba ku son junanku ba. Kareem zan baka shawara karka yarda ka rasa Yusura, na yi aure tun kurciya har yanzu na zauna da mata biyu a lokacin da mahaifiyarka take raye, mu kan samu tsabani mu yi dadi, wani lokacin har iyaye su sani, amman ban taba ganin matar aure da bata taba kuka da mijinta ba sai Yusura, bata fadin sherinka, bata kawo kararka, kai a gurinka ba abun kunya ba ne aji ka saki matarka? Kuna da yara biyu me kake fada musu? Idan aure kake son karawa you're free to do so ba sai ka saki matarka ko ka wulakanta ta ba, idan har kana fadar saboda Mahaifiyarka ka aureta to miye amfanin sakin a lokacin da mahaifiyarka bata raye? Ke nan ganin idonta kake yi ma biyayya ba saboda Allah ba? Yanzu da ban yi magana ba haka zaka zuba ido ta cika idda? Ko saki uku ka yi mata? Domin bata fada mana ko saki nawa ka yi mata ba, kuma ita bata zauna kamar kai ta kalli kwayar idonmu ta fada mana bata son dan mu ba, Kareem idan ka sake ka rasa Yusura ka rasa matar kirki kenan har abada” Kareem yayi shiru be ce komai ba, domin ya fahimci Daddy ba zai yarda da duk wani zancensa ba. “Saki nawa ka yi mata?” “Daya” Sai a lokacin Daddy ya sassauta muryarsa ya daina yi ma Kareem fada. “Ka yi hakuri, shi zaman aure dan hakuri ne, duk can talkaminmu suka tsinke, dole sai an kai zuciya nesa, bana son na sake jin wata matsala a tsakaninku, ka maida matarka dakinta ku zauna lafiya dan Allah” Kareem kamar zai fasa kuka ya ce. “Daddy mai daki shi ya san inda yake masa yoyo...” Be rufe baki ba Daddy ya rufe shi da fada yana masa tsawa. “Get out Kareem, tashi ka dauki matarka ka aje ta gida sannan ka wuce aiki, wato Momy kake tsoro kana gudun zuciyarta mu kuma ka raina mu ko? Toh ka bari har bayan raina sannan ka saketa idan ka ga dama ka hada har da yayanka ka koresu gaba daya” Da sauri Kareem ya sauko daga kan kujera yana bawa Daddynsa hakuri, domin idan akwai abun da yake gudu da tsoro a rayuwarsa to fushin iyayensa ne. “Ka yi hakuri Daddy, na maida aurena saboda kai, kuma zan dauke ta mu tafi gida yanzu kamar yadda ka ce ka yafe min dan Allah” Daddy ya dauke kai ya kai hannu ya dauki gilshinsa ya mike tsaye ya shige bedroom dinsa. Kareem ya dafe kansa ya rumtse ido, ya fi karfin minti talatin a haka sannan ya dago ya fito daga bangaren ya dawo bangaren Hajiya Hassana ya zauna a falon ya kasa yin komai har sai da Step mother dinsa ta fito sannan ya gabatar mata da abun da ya maido da shi bangaren nata. “Na maida aurena Hajiya, a fada mata ta fito mu tafi” Hajiya Hassana ta yi murmushin jindadi. “Haba yanzu na ji magana, ko kai ba haka ake so, kuma dan Allah ayi ta hakuri karka ce zaka biyewa mace ita mai rauni ce, kuma duk matsala da za a samu a daina saurin saki, muna raye idan ya kamata mu ji sai ka sanar mana mu tsawatar mata yafi ayi ta saki ga yara” “Tohm Hajiya” Ya amsa irin amsawar nan na wanda ya rasa interes da mafaka da kuma gata a lokaci daya, daman tun farko yayi tsammanin haka shi ya hana shi sakinta a lokacin da Momy bata dade da barin duniya ba, da ace kuma ya sake a lokacin da take raye Allah kadai ya san irin fushin da Momy zata yi da shi. Ya mike tsaye yana jin wani fever na rufe shi ya nufi motarsa ya bude ya shiga ciki ya zauna yana jiranta bakinciki cike fal a zuciyarsa. Ya bata awa daya a haka sannan Aneesah ta fito ta bude motar ta ce masa. “Big Bro wai Hajiya tace ka tafi zata kawo ta da kanta” “Toh ki fadawa Daddy haka idan na wuce” Cikin tsananin damuwa Kareem yake maganar sannan ya ja motarsa ya fice daga gidan. Wunin ranar aiki kawai yayi dan ya zame masa dole ba dan jikinsa da zuciyarsa suna cikin dadi ba. Bayan ya gama yana kokarin hada kayansa ya wuce wata mate room ta shigo ta kawo masa takardar envelope. “Maman Khalid miye wannan” “Wallahi ban sani ba, wata ce ta zo dazun bata same ka tace bari ta ba ni na aje maka dan Allah kar na bawa kowa sai kai hand to hand” Ta fada cikin hausarta da bata gama kwarewa ba, kasancewarta bayarabiya. Ya karba fuska ba yabo ba fallasa yayi mata godiya ya hada kayan saukinsa ya fice daga office din. Sai da ya shiga motarsa sannan ya bude envelope din wani kamshi mai dadi ya bugi hancinsa, flower ce farkon abun da ya fara cirewa daga takardar sannan wani sexy chocolate da kuma farar takardar mai rubutu red. Be yi tsammanin ganin romantic abu irin wannan ba sai a Safeena kuma ya canka daidai a lokacin da ya fara karanta sakon na karin shekararsa a yau. “Happy birthday Love, barka da zagayowar ranar haihuwar mutumen da bana son zama da kowa sai shi, barka da zagayowar ranar haihuwar mai bani farinciki a zuciya da jiki, mai kwantar da min da hankali, mutumen da ke nisantarsa ke haukata ni ta hana ni sukuni, barka da karin shekara My future husband, my partner in crime, the father of my future kids, father to be... I know its your birthday today.. I am sure u will give me treat in a big house like we use to be.. so I shall talk to you in person there, because I don't know to express my feelings in paper, i love you duk yadda kake tsammanin za mu iya rabuwa da junanmu ba zamu iya ba Kareem saboda muna son junanmu, ba zan iya kyaleka a irin wannan yanayin da kake da bukatar wani a kusa da kai ba, i know how painful it's to lost a best friend and Mother. Please take good care of yourself for me...” Ya girgiza after ya gama karantawa, so today is his birthday gaba daya ma ya manta, daman tun kamin su rabu tun tana girlfriend dinsa ita take tunawa da birthday sai kuma Momy, and even after break up bata daina wishing dinsa ba a duk lokacin da ranar zata zo. Wani gurin ya bude a motarsa ya saka takardar ya rufe ya yi ma motarsa key. Kusan wannan ne karo na farko da yake jin kamar baya sha'awar komawa gidan all his thoughts is Yusura ta koma gidan by that time, hakan ne ya rike shi daga komawa da wuri domin samawa yaransa abun da za su ci da rana wani lokacin daga restaurant yake karbowa ya je musu da shi, wani sa'in kuma da kansa yake girkawa tare da su ko kuma kamin su dawo. He park his car near the entrance ya bude motar ya fito ya shiga falon. To his greatest surprised yaransa suke tarbe shi da wani irin farinciki da murna da ba su taba tarbonsa da shi ba. “Dady welcome home, Dady Mamy ta dawo” Ya rage tsawonsa yana kallonsa da murmushin da ya ara ya yaba a fuska saboda yaransa. “Kun jidadi?” “Eh sosai” Babbar ta fada sai ya shafa kanta, ba su taba tambayarsa ina Mamy su tafi ba, yaushe zata dawo me yasa bata gidan, tun da suka dawo daga school ba su same ta ba ba su sake walwala ba, kuma ba su tambaya ina take ba, kai ka ce sun fahimci sakinta aka yi, tun daga lokacin Kareem be sake kai su family house dinsa ba saboda gudun su ganta ko kuma su yi kuka idan zai dawo da su. “I'm happy too” Ya fada yana kallonsu cike da alfahari, and he's not lie farincikin yaransa farincikinsa ne, hakan kuma ba yana nufin ya jidadin dawowar Yusura ba, idan har akwai abun da yake nadama a yanzu be wuce aurenta ba, me yasa be fadawa Momynsa gaskiya from first place ko da ba zata jidadin haka ba? Yanzu a wa gari ya waya, waye a matsala sama da shi? “Kun ci abinci?” “Eh munci Mamy ta dafa mun ci, naka yana dinning Dady” “Okay bari na je na yi wanka na shirya sannan na zo na ci, ku je ku yi shirin islamiya” “Okay Dady” Karamin ya amsa, babbar kuma sai da ta sumbance shi sannan ta nufi sama da gudu tana murna. Tsaye yayi yana kallonsu har suka haye suka shige dakin Yusura sannan ya sauke ajiyar zuciya ya haura stairs din ya shiga dakinsa. Bayan yayi wanka ya kwanta a dakin yayi bachi awa daya ya farka, bandakin ya shiga yayi alwala ya fito ya saka ya sauya tufafin jikinsa daga kanana zuwa shadda sannan nufi madubi ya dauki dan'uwansa turare ta feshe jikinsa sannan ya dauki wayarsa ya wallet dinsa then car keys ya fice daga gidan gaba daya. A hanya ya tsaya yayu sallah la'asar sannan ya karasa restaurant dinsa. Yana shigowa reception din Nabil da ya gama dutysa zai fita ya gaishe shi cike da girmamawa. Kareem ya mika masa hannu suka gaisa. “Ka gama naka eh?” “Eh na gama ranka ya dade, daman duty safe nake yau, ko akwai abun da zan yi?” “No aa, ka ce ka daina karatu?” Ya gosa kansa cikin jin kunya ya amsa domin abun kunya ne wannan zamanin a kalli matashi kamar shi ace baya karatu a . “Eh Wallahi, amman dai zan koma nan gaba idan Allah ya yarda” “Me ka taba karanta? Wane course?” “Mass Com na fara, amman dai ina son nan gaba idan zan koma na canja course” Kareem ya cigaba da tafiya yana fadin. “Why baka son aikin jarida ne?” “Ina son, amman dai yanzu na fi sha'awar Public health” “Karatun health yanzu yayi yawa, why not ka yi political science? Karatun yana da kyau, kuma idan ka dace da gurin aiki kamin an ankaro ka dauke nauyin gidanku” “To da har ka kawo wannan shawarar da yardar Allah shi zan yi ranka ya dade” Kareem yayi murmushi yana jindadin yadda Nabill yake girmamashi. “Na jidadin haka, ni kuma zan yi kokarin sama maka scholarship, a private ko kuma gov school, ban sani ba ko a samu a nan gida nigeria ko kuma a waje, fatan dai ba zaka ba ni kunya ba” Nabil ya rasa me zai ce ya rika hannun Kareem yana son masa godiya ya kasa domin be taba kawo wani zai dauki nauyin karatunsa ba, wanin ma kuma Kareem. “Ranka ya dade, na rasa me zan ce ma” “Toh ka aje kalamanka sai idan an samu tukuna, sai ka yi godiya” Cewar Kareem yana dafa kafadarsa sannan ya wuce yana murmushi ya bar Nabil tsaye da mamaki. Be yi taku goma ba ya juyo ya kalli Nabil. “Nabil ya Noor take?” Nabil ya hade yawun bakinsa da sauri ya matsa yana amsawa. “Ta.. Tana lafiya ranka ya dade” “Ba wata damuwa babu wata matsala?” “Eh to tana dai cikin damuwa, mutuwarta nan ta dan taba ta gaskiya, domin ta canja gaba daya kamar ba ita ba” Kareem be ce komai ba, ya juya ya cigaba da tafiyarsa. Office dinsa ya shiga sai da ya zauna sai kuma ya tashi yake yi yanzu a duk lokacin da ya shigo, da zarar ya kalli kujerar da Hafiz yake zama idan ya shigo office din da yamma sai ya ji babu dadi. Har yanzu ya gagara sabawa da rashin abokinsa wannan kawa zucin yana nan tare da shi, shi ke hana shi walwala a duk lokacin da ya shigo office din. Be wuce minti ashirin a ciki ba, ya mike tsaye ya dauki keys dinsa ya fice da kansa ya shiga ya saka aka zuba masa abincin da yake sha'awar ci yaron gurin ya rika masa har gurin motarsa. Front seat ya bude aka zuba abinci sannan ya rufe ya shiga bangaren tuki yaja motar ya fice daga restaurant din gaba daya. Tuki yake not knowing what to do or to go, shi dai gashi nan duniyar gaba daya ta ki ta yi masa dadi. Be faka ba sai da ya samu wasu itatuwa dake gefen hanya, ta cikin itatuwan ya ratsa ya faka motarsa sannan ya bude ya dauki abinci yana ci, gurin is so fresh ga wani iska mai dadi babu damuwa ko hayaniyar kowa it's just him and himself. NOOR POV A kwana a tashi babu wuya ga Allah, kamar jiya na fara wanka duk dai wasu sukance wankan be wajaba a kaina ba, saboda ya sake ni, sai dai zancen da ya fi karfi shi ne na yin zaman takaba domin akwai gyara a auren kuma ban kai ga cika idda ba ne ya rasu. A ranar da na yi wata hudu da kwana goma Mama ta aiko da waina da fanke aka raba sadaka yan'uwanta suka zo tare da yan'uwan Baba aka saka ni na yi wanka na saka sabuwar atamfar, a ranar kuma mutuwar Hafiz ta dawo min sabuwa kai kace mun yi shekara aru aru da shi ba yan watanni ba, sai dai abun da ya daure min kai shi ne na rashin zuwan dangi ko yan'uwansa a gurin tun a ranar da na dawo gida har zuwa yau babu wanda ya leko ni ko ya bincika lafiyata, abincin da ake cewa dangin miji ma suna kawowa matarsa idan tana takama basu kawo min ba. Wata kila Aisha ta shafa min bakin fenti a idonsu domin na lura har bayan mutuwar Hafiz kishi take da ni. Bayan sallah Isha'i, a lokacin da kowa ya watse, ina zaune ina gyara wake soya Yaya ya shigo cikin gidan da kuzarinsa ya ce. “Noor oga Kareem ne a waje yace na kira ki” Na yi shiru na wasu dakiku sannan na mike tsaye kamin na cira kafa na ji Umma ta tabe baki tana fadin. “Wannan ai ba mutunci ba ne, ace ana maka sallama ka mike kai tsaye ka fice ba tare da tunanin fadawa mahaifi ba, kai ma ai ba ita ya kamata ka samu kai tsaye ka fada mata ba mahaifinku ya kamata ka fadawa” “Ba kisan waye oga Kareem ba Umma, oganmu ne na gurin aiki kuma abokin mijinta nw Hafiz ya saba zuwa nan akai akai” Ya Nabil ya bata amsa. “Tohm Allah ya kyauta, tashi ki tafi, amman gaskiya idan haka mahaifiyarku ta koya muku ba abun kirki ba ne, ai sai uba ya aminta ake fita domin shi yake aurar da yarinya” A kam ban iya rike kaina ba sai da na mayar mata da martani. “Baki san komai akan uwarmu ba, karki sake fadin wata mummunar kalma akanta” Kallona ta yi ta dauke kai bata ce komai ba, ta cigaba da dakan yajin da take. Ni kuma na shiga ciki na dauko hijab dina na saka na fito kofar gidanmu. Sai na same shi a gurin da suka saba tsayuwa shi da Hafiz idan sun zo, ko kuma idan ya zo shi kadai. Ganinsa ya tuna min da Hafiz sosai sai zuciyata ta yi min babu dadi, shi kuma na lura baya cikin walwala da farinciki, gashi ya rame kamar ni yayi hudu haskensa ya rage. Gambun motar dake bude ya rufe sannan ya jingina da motar yana kallona kamar wanda be taba gani na ba. “Noor how are you now?” Tambayar yake ya nake, amman sai na ji kamar yace na fada masa damuwata ta hanyar kukana. Kawai sai na fara hawaye ina kallonsa, i miss him i miss his friend i miss my previous life. “Kina cikin damuwa ko?” Na daga mishi kai, sai na ji ya sauke ajiyar zuciya. “Duk yadda kike tsammanin abun ya wuce nan Noor, na fi ki shiga damuwa yanzu, i loss hope, kawai ina rayuwa da kokarin tsayawa saboda Yayana, a yanzu babu wani daki da zan iya rufe kaina na ji sanyi, duka dakunan zafi ne da su kamar wuta” Na share hawayena. “Da zan iya komawa na gyara rayuwata ta a baya...” Na ji ya fada sai kuma yayi shiru be cigaba ba. Ni kuma na kalleshi na ce. “Da ka goge shafina a rayuwarka” Ya girgiza min kai. “Ba zan iya goge ki a rayuwata ba Noor ko da kuwa ace ina da wannan damar, ba ki min komai ba, babu dalilin da zai saka na natsane ki, you're just innocent, precious soul, and Hafiz was right akan abubuwa da yawa akanki” “toh me zaka gyara?” Yayi murmushi ya gyara tsayuwarsa. “Ba wannan ya kawo ni, na zo nan ne saboda na yi magana da ke da kuma Baba, amman kamin nan fada min ya kike?” “Ina lafiya, amman mutuwa bata da dadi Kareem, shiyasa lokacin da Hafiz ya fada min mahaifiyarka ta rasu, na yi kuka sosai na tausaya maka yanzu kuma na ji yadda ake ji” Murmushi yayi ya daga kansa sama sai kuma ya sake kallona. “Noor... Kamin na manta, na zo nan ne saboda maganar gadonki da kuma kayan dakinki” Na cigaba da kallonsa ina sauraren abun da yake fada. “Noor dan Allah karki ce zaki yi jayayya da iyayen Hafiz akan gado ko wani abu, sun ce baki da gado kanensa ya kira ya fada min kuma na je na same su na yi musu magana na fahimtar da su, amman ba su yarda ba, iyakar hujjarsu wai Hafiz ya sake ki kamin ya rasu, kuma kamin ya sake ki wai be taba tarayya dake ba haka ne?” A nan na sauke kaina kasa na dan bata rai. “Aisha ta bata ni a gurin kowa, kuma ita ce silar duk faruwar haka” “Babu wanda zai iya bata ki a gurina, kuma mutuwar aure abu ne da Allah ya kaddara, kuma ba dan Allah ya rubuta haka ba, na yi magana da Hafiz kuma yayi alkawarin yana dawowa zai zo ya dauke ki ku tafi gidan tare, sai dai kamin ya iso Allah yayi ikonsa” “Da gaske?” Ya daga min kai. “Yes Noor na lura kina cikin damuwa a lokacin kuma kin fada min kina son komawa ai, babu wani abun da zaki roka ban miki shi ba Noor sai idan ba zan iya ba” “Na dauka ina takura maka ne, na ga har baka son zuwana gurinka, na san ni ina da takura ai” Yayi murmushi. “To ki yi hakuri, idan Baba yana ciki shiga ki masa magana” “Baya nan yana majalisa” “Shiga ciki zan je can na same shi, ki kwantar da hankalinki Allah zai baki abun da ba su ba ki ba, kayan dakin ma sun ce ba za su baki ba ai saboda shi yayi komai” “Ni fa ba abun da ya dame ni da wani gado, su je su yi ta riko, amman ka yi magana da Baba shi ne dai na ji yana zancen zai yi kara idan ba a bada ba” “Okay” Kallona yake har na shige cikin gidan, ina shigowa Ya Nabil ya fita waje.Duk wata maganar da zai yi da Baba na san ba zai saurare shi, amman kudi za su iya sakawa ya fahimci komai kuma ya sassauto. Da alaka kuma Kareem yayi amfani da su ne domin babu ya shigo da far'a har da tsarabar nama yayi ma Umma. Cewa yake a yanzu ya hakura zai kyalesu amman saboda Kareem be kawai ba dan haka ba da babu abun da zai hana shi jan min hakkina. Yanka biyu aka ba mu, sai da muka cinye sannan yayi mana albishir wai Kareem ya fada masa ya nemawa Ya Nabil karanta a Sudan. Farinciki ya cika ni a lokacin da Baba yake fada min Kareem yana neman izininsa idan ya aminta sai ya fadawa Ya Nabil din ya kai masa takardunsa na SSCE. Sanin da na yi ba karamin dadi Ya Nabil zai ji ba, ya saka ni farincikin da na kwana biyu ban yi ba. Hakan kuma ya karantar da ni cewar Kareem yana da kirki ta wani bangaren, domin gashi ya danne kudirin mahaifina kuma yana kokarin nemawa dan'uwana karatu alhalin be hada komai da mu ba. Farinciki a gurin Yaya Nabil ba a magana kamar zai zuba ruwa kasa ya sha domin murna, daman abun da yake nema ne yana son karatu shi da Hana ba kamar ni ba. Washe gari da safe Kanen Hafiz ya sake kawo min ziyara sai dai wannan karon ba, maganar gado ce ta kawo shi ba, ya zo min ne da tsaraba ta atamfa biyu da kuma turare sai sabulu da talkami da kudi 10k wai yana taya ni murna fita waka, kuma na yi hakuri da yadda yan'uwansa suka nuna min halin ko'ina kula. Na karba na yi masa godiya muka yi sallama na shiga ciki, bana tunanin ina da wata bukata ta kudi a yanzu wannan ya saka na dauki kudin na bawa Hana na ce ta kaiwa Mama idan ta tafi gidan, domin ita ce mai yawan zuwa ni ban taba zuwa ba domin an yi auren ne a lokacin da ba ni da halin yawo. Abu kamar wasa, shiryen shiryen tafiyar Yaya Nabil Sudan ya fara, duk wani abu da za'ayi Kareem ne yake ba shi kudi yayi, har aka kammala komai within three months. Ranar da zai je yi ma Mama bankwana na bi shi muka tafi tare, ni da shi sai a ranar muka fara zuwa gidan. Babba gida ne mai bangare kusan hudu, gida ne mai kyau da tsari Mama da kanta na san ba ta taba mafarkin aure irin wannan gidan ba. Da muka shiga ciki sai ta zame mana kamar wata bakuwarmu saboda yadda rayuwa ta canja mata, ta yi kiba ta kara haske ga tufafi masu tsada kayan kallo kai har da dinning da ac kamar daman can Mama bata taba auren talaka ba, duk inda ta wulga kallonta nake kamar wata bakauya. “Noor na zame miki sabuwa yanzu ko?” Na yi dariya ina kallon plate din taliyar da ta aje min nama batsa batsa kamar wanke. “Mama ina ta mamaki ne, ina kika hadu da wannan mutumen ne?” Ta dan hade rai. “Mutume? Toh idan ba zaki iya kiransa da Baba ba, ki kirashi da suna Alhaji kamar yadda kowa yake kiransa a gidan nan, wato ke dai sakarcin ki ba zai canja ba ko?” Na yi shiru ina kallon Yaya dake cin taliyar, sannan na soma cin tawa. Rabin abincin kawai Yaya ya ci ya sha ruwa yace zai tafi. “Da wuri Nabil na yi zaton sai dare, saboda Alhaji ya dawo ku gaisa, yana ta fadar ban taba gabatar masa da sauran yarana ba, be san kowa a cikinku ba sai Hana da ke yawana zuwa” “Bana son na kai dare Mama, akwai guraren da ya kamata na tafi kamin ba bar garin nan, kuma kin ga kwana biyu ya rage min” “To sai dai kai ka tafi Noor kuma zata tsaya sai ya dawo kun gaisa tukuna ta wuce” Mama ta shiga dakinta ta dauko masa babbar leda cike da kaya sannan ta danka masa 20k tana ta sakawa Kareem albarka wai daman a yanzu tana ta tunanin wace makaranta zata nemawa tarin kudin da take shi take yi ma, amman gashi ya dauke mata nauyi. Bayan Ya Nabil ya wuce muka zauna da Mama muna hira take tambaya ko Zafeer ya ji rayuwar Mijina. “Zai iya ji tun da iyayensa suna cikin unguwar, ko basa nan ma ai yan gulma suna nan, fitowar nan ma cewa suke ta yi hakkinsa ne” “Zafeer yana sonki sosai, zai iya dawowa yanzu ma, wata kila kuma iyayensa su hana shi, ko da yake a can baya ma sun yi ta kokarin hana amman ya nace sai ke, gashi kuma an watsa masa a ido, Wallahi mahaifinku be kyauta ba” “Baba ma da yace be yafe ba idan na sake masa magana, shi ne abun da ya fi damuna” “Wai har yanzu? Toh ai Hafiz din baya raye kuma, yanzu idan Zafeer ya dawo ba zai bari ya aureki ba?” “Ban sani ba, amman da kamar wahala saboda yana ganin Zafeer talaka ne” “Haka ne, ubanki be ji wani yare sai na kudi, gashi babu mai iya ja masa liyi a dangi komai yayi daidai ne a idonsu” Na daga kai ina kallon POP din falon. “Taso mu tafi ki gaisa da mutanen gidan, suna ta tambayar, da kika fita wanka ma sai da matarsa tace zata tafi ta duba ki kuma Allah be yi ba” “Ita bata kishi ne Mama?” “Ana tabawa mana ayi mace babu kishi, amman boyewa ake na ciki na ciki, ita dai tana da kirki ba kamar wasu ba” “Ko dai irin na Aisha take miki ba, haka take nuna min ba komai ashe wayo take min” “Ke dai da halinki Noor, na san ki ba, kuma zamanmu a nan Alhaji ya fada mace kamar riga take a wuyansa duk wanda ta daga masa hankali cire ta kawai zai yi ya aje, duk tarin yaransa babu wanda uwarsu take cikin gidan nan, sai wannan matar da yaranta uku, sauran duk iyayensu sun fita, ni ma sai bayan auren nake ji, wata kila shiyasa ta kama kanta” Ina jin haka na san an gudu ba a tsira ba ne, kenan ita ma idan ta yi masa ba daidai ba zai iya sakinta. Daga bangaren Mama muka fito muka shiga bangaren matar da take gidan a yanzu. A cike muka samu falon da mata da maza, Mama ta yi sallama suka amsa suna gaisheta da mutunci. “Noor Ya hakuri?” Wata budurwar da ban waye ta ba ta fada sai na amsa da Alhamdullahi na gaishe da Hajiyar. “Lafiya Kalau Noor, an fita wanka ko? Tohm Allah ya bada hakuri ya kawo na gari” Mama ta amsa da Ameen. “Alhaji ne be santa ba sai mita yake ina boye masa yara, tare da yayanta take jibi zai wuce Sudan gurin karatu, ya zo bankwana amman be tsaya ba, ita kuma ba ce ya tsaya ta gaisa da yan gida” “Ta kyauta gaskiya, da ma dai kin maido nan kila zata fi jin sanyi kin san gidan na mu cike yake da mutane” “Mahaifinta ne ai be yarda ba, ko takaba a nan ya so ta yi amman uban yace ba zata yi ba” “Kin san wasu mazan akwai kishi” Haka dai suke ta hirarsu ni dai kaina na kasa ban dago har sai da na ji an bude kofar falo alamar mutum ya shigo. Dagowar da na yi sai muka yi ido hudu da Safeena tana dauke da cikinta da be gama girma ba. Bata kallon kowa sai ni ni ma kuma bana kallon kowa sai ita muka rika kallon kallo wata kila ita ma tana mamakin ganina ne kamar yadda nake mamakin ganinta. Gidansu ne? Ko kuma zuwa ta yi? Ko kuma dai tana da wata alaka ce da mutanen gidan? “Kin dawo Safeena?” Hajiyar ta fada sai Safeena ta amsa mata ba tare da ta kalleni ba, har lokacin ni take kallo. “Na dawo Hajiya, na karbo files din gobe zan tafi asibitin na kai” “Toh Allah ya taimaka ya raba lafiya” “Ameen” Ta amsa sannan ta dauke idonta ta zauna a kujerar dake facing dina, sai kuma ta sake dasawa daga inda ta tsaya. “Anty Safeena kin santa ne?” Na kalli mai tambayar wata kila su ma sun lura da kallon da take min yayi yawa. Ga mamakina sai ta amsa da cewar “Aa ban san ta ba, wacece hala? Ta yi min kama da wata kawata ce ta yarinya” “Noor ce yar wajen Anty Amarya, wanda mijinta ya rasu” “Allah sarki Allah ya masa rahama” Ya juya tana kallon Mama dake amsawa da Ameen sannan ta sake kallona. Har muka baro bangaren babu abun da take sai kallona kamar wata bakuwarta. Ban kuma san dalilinta na boye cewar ta san ni ba. A bangaren Mama na koma na zauna har dare ina jiran dawowar mijinta saboda mu gaisa, be shigo ba sai bayan Magariba a lokacin da ake hada hadar Sallah Isha'i. Na yi mamakin yadda yayi murna da farinciki ganina babu wata kyama, har na na yi sha'awar ina ma ace shi ne mahaifina ba Baba ba, zaunawa yayi a falon yana ta min nasiha akan hakuri da rayuwa na halin da na samu kaina da kananan shekaru, na yi masa godiya ya saka hannunsa aljihu ya ciro 10k ya ba ni. “Aa na gode” A bakin gaskiya ta ba zan karba ba, domin ko na karba ban san miye zan yi da su ba a yanzu. Sai dai na lura hakan be masa dadi ba domin rufe ni yayi da fada a dole na karba na yi masa godiya. “Tafi bangaren Hajiya ki ce na ce cikin yaran nan duk wanda yake nan ya sauke ki gida” “Tohm” Na mike tsaye na yi ma Mama sallama sannan na fice daga falon yana ta kallona. Bangaren Hajiyar na dawo na sanar mata abun da Alhaji ya fada sai mutumen dake tsaye a gabanta yayinda take zaune ya juyo ya kalleni. A nan ma wani mamakin ya kara kama ni, mutumen nan da ya taba yunkurin biya min kudin siyayyar da na yi a wani dare da muka fita tare da Hafiz. “Kamar na sanki?” Na bude baki kamar zan yi magana sai kuma na yi shiru, ban san me zan ce ba, ni dai ina da saurin gane mutane shiyasa na gane shi. “Noor ce Yar wajen Anty Amarya ce, ita ce wadda mijinta ya rasu” “Ai ban sani ba, Allah ya jikanshi da Rahama” “Ameen, ku tafi tare sai ka sauke ta ka wuce, Noor bari ga Abdull zai fita yanzu sai sai ya wuce da ke, ki jira shi a waje” “Okay” Na juya na fito daga ciki, ban san wacece motarsa a cikin motocin gidan ba dan haka zauna a balcony har ya fito. “Kika zauna a kasa?” Bance komai na na mike tsaye na bi bayansa muka isa gurin wata sabuwar mota, sai da ya fara shiga sannan na bude na shiga front seat. Ba tare da yace min komai ba yayi reverse ya fice daga gidan. “Ina ne unguwarku?” A lokacin da na dago sai na ga idonsa akaina suke. Na fada masa na sake maida kaina kasa kamar ba ni ba. Na ji lokacin da wayarsa ta yi kara ya amsa. “Hello Safeena...” Sai kuma yayi shiru, yana sauraren abun da ake fada masa. “Yanzu na fito gida, amman zan biya ta can, sai na zo miki da shi, shi kadai kike so ko da wani abun?” Na yi shiru ina saurarensa kamar wata Munafuka kamin na ji ya ce. “Okay sai na dawo” Ya aje wayar ya dago zan kalleshi idona suka fada cikin nasa da sauri na dauke kaina ina jin sautin murmushinsa. Ban sake kallon gefen da yake ba har muka isa unguwar. “Ka sauke ni a nan unguwar bata da kyau can ciki” Na fada. “Karki damu, amanarki aka ba ni sai na kai ki har gida” Yadda ya fada haka ya aiwatar har kofar gidanmu ya isa da motarsa ya faka, ni kuma na bude na fito zan rufe kofar ya ce. “Ba godiya” Ban ce masa komai ba na rufe motar, na gode masa sai ka ce rokonsa na yi ya kawo ni. Sai da na shiga gida sannan na ji motarsa ta bar kofar gidan. KAREEM POV. Yana gama sallah asuba ya shiga kitchen hadawa yaransa breakfast. Domin Yusura bata musu komai tun da ta dawo gidan, Kullum shi zai hada musu breakfast ko kuma ya saka aika musu daga restaurant dinsa kamin su tashi break. And now cooking is one of his favorite things, yana samun nishadi a girkin, musamman idan yaran suka farka suka same shi a kitchen suna hayani yana aikinsa har ya gama, ya karya tare da su wani sa'in kuma ya zuba musu na su, ya tafi da nasa a office ko kuma su su tafi da na su school shi kuma ya ci a gida. Idan ya fita sannan Yusura take saukowa ta gyara ko'ina ta dora na rana. Tun da ta dawo gidan be taba leka dakinta ba, be taba ce mata uffan ba, ita ma kuma bata bari sun hadu ba, da zarar ta ji motarsa ko ta san lokacin dawowarsa sai ta shige dakinta. Yau ma sai da ya raka su har gurin bus sannan ya dawo ya zauna ya ci nasa breakfast. Bayan ya gama ya mike tsaye ya shiga dakinsa yayi wanka ya shirya cikin kananan kaya ya fito yana rike da lab coat dinsa da wayarsa sai kamshi yake zuba. Yayi kyau sosai ramar da yayi ta kara masa kwarjini da haifa. Sai da ya fice daga falon sannan Yusura ta sauko a zatonta ya fice gaba daya, dinning ta nufa ta tsaya tana kallon kayan karyawar da ya shirya, biredin da ya gasa ta dauka taba tabe baki ta shinshina ta aje. Sannan ta ja kujera ta zauna ta bude flask din ruwa zafi, a daidai lokacin Kareem ya turo kofar falon ya shigo domin daukar wallet dinsa da ya manta a dakinsa. Kallo daya yayi ma gurin da take zaune ya dauke kai ya haura sama ya dauko wallet dinsa ya sake fice. Yusura bata taba jin kunya irin ranar ba, bayan amincewa da aurensa da ta yi wannan ne abu da na biyu da take bakinciki a rayuwarta, ji ta yi kamar ta fasa komai na gidan dan bakinciki. Tuki yake a hankali har ya isa asibitin, ya faka motarsa a gurin da aka rubuta Dr Kareem sannan ya fito ya dauki kayansa ya rufe motar ya shiga cikin Babbar asibiti ana miko masa gaisuwa yana amsawa. Office dinsa ya shiga ya fara duba takardun dake gurin sannan ya fita ya fara duba marar lafiyar da aka aje da ya kamata ya duba su. After ya gama ya dawo ya zauna a office dinsa patient din dake shigowa suka fara shigowa yana dubata. Third person da ta shigo ita ce Safeena, tana sanye da dogon Hijabinta har kasa sai dai hakan be boye cikin dake jikinta, har ta zauna ita yake kallo. Sai da ta aje jakar dake hannunta sannan ya jingina baya ya kwanta jikin kujerar yana kallonta. “Wai ke wace irin yarinya ce Safeena?” “Ni din wata yarinya ce, mai wuyar warke ciwo, wata yarinya ce da ka koyawa soyayyarka kuma kake kokarin guduwa bayan ka yaudareta da farko” “Gargadin da na yi miki, da kuma tazarar da na baki daga lokacin da muka yi haduwar karshe zuwa yau bata fahimtar dake, na rumgumi kaddarata, ke ma ki rumgumi taki?” “Ka rumgume kaddara saboda Yusura tana sonka tana kyautata maka a yanzu? Ko kuma daman can karya ka yi min kace bata kula saboda kullum ka rika samun biyan bukatarka da ni? Ka yi breaking heart dina da farko yanzu kuma bayan na saba mu'alama da kai na saba da kwanciya a kirjinka na saba da soyayyar kake tunanin sake guduwa ka bar ni?” Ya mike tsaye daga zaunen da yake ya nufi windows dinsa ya bata baya. “Kana da kyau, Kareem kana da kudi amman duk wannan be tabbatar min da ina sonka ba sai da mu'amala ta hada mu, all this while na kyale ka ne saboda ina dauke da cikin nan” “Me kika zo yi yanzu? Tashi ki fice daga office din nan” “Baka da wannan damar ba saboda da kai na zo ba, saboda cikin nan ne, na dawo da awon cikin nan a nan ne, a nan zan yi ta zuwa har zuwa lokacin da zan haihu” Ya dafa Window ya rike kansa. “Namiji zan haifa suka ce, kuma ina alfahari da haka” Kareem ya dauki lokaci a haka kamin wani tunanin ya zo masa sai ya juyo da sauri ya kalli cikin na ta sannan ya kalli fuskarta, sai ta yi masa murmushi. “Fita ki bar office din nan” Ya nuna mata kofar, zata sake magana da daka mata tsawa har sai da ta zabura. “Fita ki bar office din nan na ce” Ta mike tsaye da sauri ta dauki jakarta tana kallon yadda ya hade fuska kamar be taba ganinta ba, ta fice daga Office din. Dawowar yayi ya zauna kan kujerar ya dafe kansa ya runtse ido yana numfashi da karfi, ya girgiza kai kamin ya daga hannunsa ya buga a tebur din yana jin wani irin bakinciki marar misaltuwa... It could be a joke maybe tana gwada shi ne, if not ai tana da hankali matukar ba wata manufa take da ita akansa ba ba zata taba sha'awar haihuwa da shi alhalin tana da aure ba, ta dauki dawainiyar cikin da ba na mijinta ba ta kai masa yayi komai, ba zata fara ba. Abun da zuciyarsa ta raya masa kenan har ya ji ya samu saussaucin cigaba da aikin da yake. Sai da lokacin tashi aikinsa yayi ya tuna da ba shi da abokin hira ko shawara a yanzu domin Hafiz is no more balle ya fada masa hasashensa ko damuwarsa.Tafiyar Ya Nabil karatu ta zame ta bude min wani gurbi a gidan. Domin ruwan da yake debo mana da safe yanzu nauyin ya koma kaina, ni nake cika gidan da ruwa ga jikin nawa ba mai son wahala ba ne amman haka nake daurewa ina yi saboda gujewa hayaniyar Baba bana son ya jefe ni da wata kalmar marar dadi a yanzu. Haka ma ba fita nake son yi ba, saboda idanuwan mutane yana kaina, idan na hadu da kanen Zafeer har jefa min magana suke kamar ni na so mutuwar auren ko kuma zaman gidan. A haka dai na daure na danne zuciyata ina cigaba da rayuwa a gidan ubana. Ranar wata labara Anty Larai ta kawo mana ziyara har da tsarabarta domin ta dade rabonta da gidan. Rabon da na saka a ido kuma tun a gurin gaisuwar Hafiz. Na yi murna sosai da ganin tana cikin Gwagganina masu hankali da kamanta adalci daidai gwargwado. Ina zaune kusa da ita nabban danta Ridwan Wanda ya kasance cousin ne a gareni sai tsokana ta yake, ni kam baki ya mutu bana cewa komai, Hana ce take ramawa sai Umma dake dan jefo magana sama sama. Gwaggo ta shafa kaina zuwa bayana tana murmushi ta ce. “Ka bi ka saka min yarinya a gaba, saboda yanzu ka samu ta yi lafiya ko? Da ada ne ai ba zaka iya da ita ba” “In ji waye ko a da ne zan iya, kawai ina daga mata kafa ne” Anty Larai ta bude jakarta ta dauko goro ta gutsira tana fadin. “Nabil an tafi ko? Ya zo min bankwana ai, Allah yasa ayi karatu cikin nasara” “Ameen” Na amsa ina daga kai na kalli Ridwan dake shirin tafiya. “Zaki dare nan?” “Aa idan dai ka yawato ka samu abun da zaka samu sai ka dawo ka dauke ni mu tafi gida” “Yaya Ridwan har yanzu Napep din kake ja?” “Toh ya za'ayi abincin a nan yake” Ya amsawa Hana dake tambayarsa domin tun tashinmun, Yaya Ridwan ba shi da wata sana'a da ta wuce jan Napep, da ita ya rike gidansa ya yaransa da matansa biyu har ma da mahaifiyarsa. “Allah ya taimaka” Cewar Umma, dukanmu muka amsa da Ameen sannan ya fice. Shimkafa da miya Umma ta girka saboda zuwan Anty Larai, bayan mun ci mun yi sallah Hana ta dauki awara ta fice gurin sana'ar da ta zame mata dole, ni kuma na zauna da Anty Larai muna ta hira, a cikin hirar nake gutsura mata irin zaman da muka yi da Aisha da yadda yan'uwansa suka jajirce ba za su ba nu gado ba. “Daman can Allah ya gani, zuciyarta bata natsu fa yarinyar nan dari bisa dari ba, mata makircinsu yana da yawa, ke kuma ba wayo ne da ke ba kuma babu mai tsawata a tare da ku, dama ace irin gidanmu ne da muke hade kin ga wani abun ko dan ganin idon uwar miji dole a bar shi” “Ni kadai nake zaune kuma kowa da bangarensa, amman hakan be hana ta cutar da ni, gashi ya yarda da ita, komai aka fada masa akanta baya yarda” “Ki barta da Allah, yanzu ai mai rabawa ta raba, Allah ya ba ki na gari ita kuma sai ta je can ta karata” Na yi shiru ina zane a hannuna da karen tsintsiya, kamin na kira sunan Gwaggo. “Anty Larai” “Na'am Khadijatu” “Anty Larai, alfarma nake nema a gurinki, na san Baba yana jin maganarki, dan Allah ki roka min shi yayi hakuri yace ya yafe min na yi magana da Zafeer” Na kora bukatar tawa ne ba tare da na kalleta ba, domin ina jin nauyin kallon idonta a yanzu. “Zafeer din ya dawo ne? Aiko ya kai masoyi kuma lallai yana sonki da gaskiya bawan Allah nan” “Be dawo ba, yana da zuciya sosai wata kila ba zai sake sona ba har abada, amman ni ina son a duk lokacin da na ganshi ko kuma na samu dama na masa bayanin da zai gamsar da shi cewar ba wai na ki aurensa saboda ba shi da kudi ba ne, na lura yan'uwansa har yanzu ganin suke kudi na bi na bar Zafeer” “Idan har yana sonki da gaske zai dawo, ai mai sonka be ganin ramar ka, be ganin tsufanka, kuma shi ma mahaifinku ai be dace ya shata muku layi mai kauri irin wannan ba, saboda zuciya bata da kashi” “Dan Allah ki masa magana, yace ya yafe min” “Zan mishi magana idan ya shigo, noor har yanzu kina son yaron nan ko?” Na daga mata kai ba tare da boye ko jin kunya ba, zan iya fadar ina son Zafeer a gaban, duk kuwa da na san a yanzu yayi min nisa. Sai na ji ta yi dariya tana buga bayana. “Aiko da har ina cewa Ridwanu ya shigo ko Allah zai ba shi sa'arki, sai ayi tuwona maina tankaden bakin gado?” Murmushi ne kadai abun da zan iya yi na kwanci kaina a wannan lokacin kuma shi na yi, sai dai ko kadan manufar da take son isarwa a gareni ba mai yiyuwa ba, sai idan cilasta Baba zata yi yayi min auren dole. Baba be shigo gidan ba, sai da yamma liss ya dawo a gajiya. Na debi ruwan wanka na kai masa yayi wanka ya fito ya zauna kusa da yar'uwansa yana cin abinci suna gaisawa. Ina alwalar magariba na ji tana yi nasa maganar Zafeer. “Ai wannan duk da ne, yanzu kam komai ya wuce, ko lokacin da na yi mata wannan furucin ta fusata ni ne shiyasa kuma na lura a wacan lokacin tana son ta biyewa zugarsa ne ta bijirewa umarnina, amman yanzu komai ya wuce” “Duk da haka dai ka ce ka yafe ka san bakin iyaye lalle ne” “Haka ne, toh na yafe Yaya Larai kina shagwaba Noor” Ta yi murmushi ni ma murmushin na yi ina jindadin janye takukun da Baba yayi tsakanina da Zafeer. Daki na shiga na yi sallah bayan na gama na fito na yi ma Anty Larai godiya a lokacin Baba yana masallaci. Shigowar Ridwan da mintuna kadan Baba ya dawo daga masallaci suka gaisa Ridwan yayi masa alheri sannan ya fita waje jiranta. Ni kuma na yi mata bankwana Baba ya rakata har waje suna tafe suna hira har suka fice daga gidan. Hana na shigowa na labarta mata cewar Baba ya daga min kafa a yanzu, yace ya yafe min na yi magana da Zafeer, na yi zaton zata taya ni farinciki ne kawai sai na ji ta fashe da kuka marar sauti. Hankali ya tashi da sauri na dafata na dago kanta. “Hana lafiya?” “Na gaji da rayuwar gidan nan Noor tun da Mama ta tafi ba mu da jindadi babu walwala, zuwan Umma ya kara mana matsuwa kuma ban mu isa mu yi magana ba, ni ban taba talla ba, sai wannan karon idan na fita da la'asar ba zan dawo ba sai bayan Isha'i dole sai na siyar da komai idan ba haka ba idan na dawo sai ta fara fada tace keta nake son mata. Baba kuma ba zai shigar mana ba sai ita, kawayena a yanzu babu mai talla sai ni, maganar nan har ya kai makarantar mu na boko, gashi yanzu mun fara jawaba, muna karewa zata oya kirkiro wani abun da zai hana ni zaman gida da safe, yanzu kina gani yadda karatun addini na bar shi saboda tallar nan, gaba daya rayuwar gidan nan ta isheni Noor ji nake kamar na gudu” Tausayinta da kuma na kaina ya kamani, idan har ita zata fadi haka to ni nace me, kashi uku na ukuncin rayuwarta data gidan Hana bata shiga daya ba, domin ita har yanzu bata kula kowa ba balle a rabata da wanda take so kamar yadda Baba yayi min. Bata yi aure ba balle ta hadu da kishiya irin Aisha wani abun na rayuwar har yanzu bata san ya zafinsa yake ba. “Ya muka iya? Tun Mama tana gidan nan muna cikin takurawar Baba balle kuma yanzu da bata nan, ni ina ganin idan kin kare karatunki kawai ki koma gurin Mama ki zauna, za ki jidadi kuma mijinta da take aure a yanzu yana son mutane ba kamar Baba ba” Ta kalleni hawaye na mata zuba. “Amman kina ganin Baba zai yarda? Ba zai yarda?” “Me zai hana idan ma be yarda ba ki yi ma Anty Larai magana zata saka baki, kin san kuma Baba yana jin maganarta” Ta fara share hawayenta. “Allah yasa” Ta mike tsaye ta cire hijabinta ni kuma na tashi na fita waje gurin aikin gyaran wake da nake kullum da dare. Tiya uku na zuba a tray na shimfida matacciyar tabarmarmu na zauna kamin na saka hannuna a waken wani yaron unguwarmu ya shigo wai ana sallama da Noor. “Je ka ce waye?” Umma ta ba shi umarni yaron ya juya ya fita. “Gashi Malam baya nan balle na ce a nemi izini gurinsa, yaran yanzu kuma ba natsuwa ce da su ba, musamman zaurawa” Tana maganar tana kallo, wata kila so take na yi mata ba daidai ba ta fada min ba dadi ko kuma ta hada ni da Baba, idan ba haka me miye na cin fuskar, ita ba zarwacin ta yi ba kamin ta auri Baba, su zaurawan dabam suke da sauran mata.? “Sallamu Alaikum, ya ce wai wanda ya saba zuwa” Ina jin amsar yaron zuciyata ta raya min Kareem ne, wata kila ita ma ta fahimci hakan shiyasa ta ce na tashi na tafi bayan ta gindaya min sharadin kar na jima saboda gyaran wankenta. To me ya zo yi kuma wannan karon? Biyo yayi ya duba ni ko kuma dai wata matsalar ce ta taso daga bangaren iyayen Hafiz da na tattara lamarinsu a gefe na aje. Bakuwa mota ce da ban taba gani ba mai bakin gilashi baka ganin wanda ke ciki duk da kasancewar akwai hasken lantarki a lokacin. Tsaye na yi ina jiran Kareem ya bude motar ya fito, sai akasinsa ya fito, mutumen nan da na taba haduwa da shi a mall kuma shi ne dai wanda ya dauko ni daga gidan Mama ya kawo ni gida. “Hajiya Nooriya kin yi mamakin ganina ko?” Toh ko dai yayi arba da mamakin a fuskata ne shiyasa ya ke tambaya. “Eh gaskiya na yi mamaki, ban yi tsammanin kai zan gani ba” Na fada ina rumgume hannayena. “Akwai wanda kike tsamanin zuwansa kenan, kar fa bazawarin ya tarar da mu ya dauka soyayya muke yi, yayi fushi” Na yi murmushi feeling Speechless daman mi zan ce bayan shi ya zo shi ya kamata yayi magana ai. “Well kawai hanya ce ta biyo da ni, sai na tuna i have a friend here na ce bari na biyo just to say, hope ban yi laifi ba?” “Are we friends daman?” Tambaya nake a bakin gaskiya ta domin ban san wata rana da muka zama kawaye ko abokai ni da shi ba. Da alama kuma tambayar tawa ta ba shi dariya har sai da ya bayyana hakoransa. “Uhm ba ma bukatar request ai, idan ba mu zama abokai ba mun zama yan'uwa saboda Mama ko?” “Maybe” Na fada ina dan wara ido. “Not maybe, pretty gal ban da jan aji, ko da yake kamata yayi na gabatar da kai ne, taya za ayi abota ba a san juna ba” Ya miko min hannunsa. “I'm Abdull by name, engineer ne ina zama a Lagos for now, ko da yake ni dan garin Kano ne haifaffen garin kano aiki ne ya kai ni Lagos kuma idan na tafi na kan yi wata biyar hudu uku har fi a can, am ina da mata da yara uku a yanzu” Kallon hannuna nake wata kila dai ya manta da cewar ni da shi hausawa ne kuma musulmai, idan ba haka ba miye na miko min hannu mu gaisa. Kareem ne kadai ya taba yi min haka bayan shi kuma bana jin akwai wanda zai sake miko min hannu na karba. “Nice to meet you Abdull” Na amsa ba tare da na ba shi hannun nawa ba. “Ba zaki gaisa da ni ba?” “Ba ayi min wannan hallacin ba tukuna” Yayi murmushi tare da maida hannun nasa. “Daman dai na zo na gaishe ki ne, hallaci kuma za'ayi miki nan gaba kadan, abu na karshe bana bukatar ki fada min komai a kanki na tambayi Mama wacece ke ta fada min yadda kike da kafiya da rashin magana, ban yi mamaki ba kuma saboda kina da kyau kin san mata masu kyau suna da rashin magana sosai” Na yi murmushi kadan, sai ya bude motarsa ya dauko leda ya mika min. “Ga tsaraba ki shiga da shi gida” “Aa na gode” “Mu ai ba ma yin kyauta a mayar mana, ko dai ki karba ko na aje miki na tafi” Jin haka ya saka na kai hannu na karba, na yi masa godiya na juya sai na ji ya kira sunana. “Noo oor” Na juyo. “Yaushe zaki je ganin Mama?” Sai da na yi nazari kamin na amsa masa. “Friday” “Okay see yeh✌” Ya sara min da yatsu biyu sannan na yi masa murmushi as responsed sannan na juya na shiga gida. Gudun laifi ya saka na aje ma Umma ledar da ya ba ni ba tare da na bude ba. “Shi ne abokin mijinki?” Bana son dogon zance dan haka na amsa mata da eh ina kallon turaran da take fitarwa da man shafi masu kyau. “Ko dai son ki yake?” “Aa daman tun kamin na san Hafiz din na san Kareem” “Toh bari a aje idan mahaifinki ya dawo sai a nuna masa” Akan haka muka rabu, ban sake ganin ledar kayan ba sai washe gari bayan Baba ya fita ta miko min ledar wai ita ta dauki turare daya Baba ya dauki biyu sun dauki man shafi biyu suka bar min daya. Ban ce komai ba na karba na shiga da shi dakinmu na aje ma Hana man shafin da turare daya na dauki dayan da ya rage. Sai da na dan kimtsa sannan na fito sanye da hijabina, kamshi kam kai kace gidanmu ake kamfanin turare na fesa wanda Abdull ya kawo min sosai saboda yana da dadi da saka sanyi zuciya. Tsakar gidan na fito na dauki bokiti uku da nake deban ruwa da su na fice daga gidan domin yin abun da ya zame min wajibi. Fanfon da muke dibar ruwa irin wannan ne mai tuka tuka sai ka yi ta bugawa kamin ya cika, haka na yi ta wahala ni kadai ina jan karfen yana jana har na cika. Da kuduri biyu na fito daga gida, kudirin debo ruwa da kuma ziyarar gurin da na san Zafeer yana aiki, domin ban isa na tunkari gidansu da bukatar ganinsa ba. Idanuwa kaikaiyin ganinsa suke, zuciyata tana ta muradin mai sakata farinciki, na san ba zai kalleni ba idan ma yana gurin ba lallai ya sake kaunata ba, amman ni zan ji sanyi idan na yi magana da shi ko da kuwa zagina yake. Tafiya ce mai dan nisa haka na kama hanya ina tafe ina ta sake saken yadda zan fara masa magana idan ma na sameshi a gurin. Na tarar da Ogansa a gurin muka gaisa yayi min gaisuwar Hafiz, kana kuma ya sokeni da wata kalma mai daci. “Noor kin guje mana ko? Duk soyayyar nan da muka nuna miki sai da kika butulci mana, gaskiya ban jidadi ba kuma na yi mamaki sosai, Wallahi ba karamin damuwa kika jefa Zafeer ba” Na aje numfashi a muhallinsa ina jin yadda bakinciki ya fara yawo a zuciyata. “Gurinsa na zo ko yana nan?” “Kai ai Zafeer ya bar nan, tun a lokacin da kika yi aure yace ba zai iya zama garin nan ba, kwanan baya dai ya zo, amman ya koma gaba daya ya kwashe komai nasa a nan, shi ma kuma Allah yayi masa sakamako na alheri yar wani babban mutum zai aura karshen watan nan In Allah ya yarda” Indai abun da nake ji a yanxu, irinsa Zafeer ya ji a lokacin da na yi aure na bar shi, tabbas ya shiga tashin hankali, kasa rike kaina na yi har sai da na fasa kuka sai kuma na yi hanzarin rufe bakina, hawaye suke Noor yau ma muna sha'awar yin ado a fuskarki. “Haka daman abun Allah yake, lokacin da wani ya ƙi ka da wuni, wani zai ya so ka da kwana, yadda kika guje masa kika auri mai kudi, shi ma Allah ya ba shi yar masu hannu da shune, yar babban mutu kuma babbar ma'aikaciyar banki, an yi lokacin da take kawo gyara a nan, bata duba talaucinsa ko kaskancinsa ba ta aure shi” “Baka san komai akaina ba oga Lawal dan Allah karka yanke min hukunci” Na fada ina hawaye, na cira kafa daker ina tafiya kamar wata tsohuwa. Har na iso gurin bohol din hawaye nake, zuciyata zafi take wasu abubuwa nake ji a cikin kaina suna min yawo. Ban tarar da ruwan da bokitan da na kawo ba, daga ruwan har bokitin wanda ya fi ni so yayi awon gaba da su, wani mai dan hali mai son biya lahira. Bana cikin yanayin da zan iya shiga gidajen da suke kusa da Bohol din balle na tambaya ko sun ga wanda ya dauka ko kuma sun dauko. Sai kawai na nufo gida ina tafe ina hawaye har na iso. “Ina ruwan?” Umma ta tambaya tana daura dankwalinta. “An dauke kayan” “Garin ya? Taya kika yi sake har aka dauke kayan? Sai kuma ki dawo min gida kina kuka, Wallahi ko kije ki nemo min kayana ko kuma na fadawa mahaifinki idan ya dawo wannan ai keta ce da sheri, kamar ya an dauke kayan kina aikin me aka dauke? Kukanki ba zai kwace ki ba” A zatonta ina kuka ne saboda an dauke kayan, bata kukan bakinciki nake ba wanda ya fi na sata ciwo. Dakinmu na shiga na dauko dubu goma da Alhaji ya ba ni a lokacin da na tafi gurin Mama na cire 1k na mika mata saura. “Ga kudi ki siya wasu” Sai da ta gama kallon kudin baki sake sannan ta karba bata ce min komai ba ta shige dakin Mama wanda ya zama dakinta a yanzu. Ni kuma na sa kai na fice daga gidan, bana iya daga kai saboda bana son kowa ya ga idanuwa. Ina isa titi na tari Napep na hau na fada masa inda zai kai ni, domin ba ni da gurin zuwa yanzu da ya wuce can. Ko da yake idan ma na tafi ban san me zan fada mata ba, ba lallai ne ta ji yadda nake ji ba, ni kadai nake iya fahimtar kaina. Bayan na sauka na ba shi dubu daya ya ba ni canji na nufi gate din dake bude na shiga, a lokacin ne wata motar ta iso kusa da gate din zata fice. Daidai saitin da nake tafiya mai motar ya tsayar ya sauke gilashin kasa. “Noor kika ce min sai friday?” Na kalleshi Abdull ne a cikin motar yana sanye da facing cap. Ban ce masa komai ba na nufi bangaren da Mama take. Ina tana kofar na jita a rufe na fara kwankwasawa. “Bata nan fa ta fita” Na juyo na kalleshi sai ya saka hannayensa aljihu ya cire hular kansa yana kallona. “Sai dai ki shiga bangaren Hajiya” “Aa ba sai na shiga ba, zan koma gida kawai” Na fada ina mamakin Hajiyar mahaifiyarsa ce ta Safeena tsakanin shi da Safeena gidansu waye ne? Ko kuma shi da ita Yaya da kanwa ne oho. “Okay Let me drop you off Girly” Ban masa musu ba ya wuce gaba na bi bayansa har muka isa gurin motar na bude na shiga, shi ma ya shiga yaja motar muka fice daga gidan. Tafiyar kamar ta kurame haka ta zama bana cewa komai sai tunanin Zafeer nake da irin rayuwar da yake ta fada min zamu yi. Ban ankaro ba na ji hannunsa a cinyata yana shafa ni. “Kin yi shiru baki cewa komai Noor” Na yi saurin buge masa hannu. “Miye haka?” Sai yayi murmushi. “I'm sorry daman ina gwadaki ne kawai” “Gwada ni kamar yaya to see what?” Asking with little bit of confuse. “To see if you're wife material...” “Sauke ni a nan” Ya dube ni da sauri. “A nan?” “Eh a nan zan sauka” “Ba gidanku ba ne ai” “Na ce ka sauke ni a nan zan sauka” Wata kila bakin hadarin da na hada a fuskata ya firgita, domin na daure fuskar sosai babu alamar wasa. A dole ya faka gefen titi ni kuma na bude na fita na bar masa motar a bude. “Kin ga ni fa gwadaki ne kawai nake ba wani abu ba...” Ban kula shi ba na cigaba da tafiya a kafa, ya so gwada bina a motar yana min magana da ya lura ba zan saurare shi ba kuma ba ni da niyar shiga motar sai ya motarsa yayi gaba. Tsaye nake ina jin kamar na fasa ihu na fadi na yi birgima a guri. Kusa da ni wata motar ta tsaya wannan karon ina ganin wanda ya fito motar sai na ji sabon kuka ya taso ni gaba, wani irin shagwaba da narkewa na fara yi kamar wata yar baby. “Me ya faru? Me kike yi a nan?” Ya tambaya tun kamin ya karasa fitowa daga motar, matsawa na yi kusa da inda ya faka motar ina kuka har da shessheka. “Kareem...” Ya kalleni hankali a tashe. “Me ya kawo ki nan Noor waya taba ki?” “Kowa ma taba ni yake...” Ya kama hannuna ya ratsa da ni ta cikin wasu itatuwa da ke gurin muka shiga ta can ciki gurin da ke da sanyi da iska mai dadi, sakin hannuna yayi. “Fada min me ya faru?” Na daga kai na kalleshi kawai hawaye na sauko min. Cikin kwantar da murya da lallabawa ya ce “Can i be your best friend?” Na daga mishi kai. “Okay daga yanzu na zama best friend dinki, yanzu fada min damuwarki” I don't know why, how and when, i just find myself laying on his chest idanuwa na zubar da kwalla. “Zafeer zai yi aure Kareem...” Mun dauki 12-seconds a haka, ni da shi babu mai motsi kamar mun mutu, but zuciyata na bugawa da wani irin karfi kamar yadda nake jin tasa ma tana bugawa, sannan ya matsa baya hakan ya saka dole na dago daga jikinsa, he look straight into my eye ball ya ce. “Noor ki daina saka turare mai yawa haka idan zaki fita, Haramun ne” “Kai turaren ne damuwarka?” “Saboda yana dagawa mutane irina hankali turare is my weakness, my weak point” Ban gama fahimtar abun da yake fada ba, na ganshi slowly yayi kasa ya zauna akan turbaya ya nade kafafuwansa ya dago yana kallona. “Zauna karanta min damuwarki, maybe zamu iya solving matsalar...” Na zauna a gurin ina fuskantarsa da irin zaman da yayi.....Kareem ya sauke numfashi mai nauyi. “Daddy, akwai abubuwan da ni da ita muka boye ba mu bar kowa ya sani ba, ban san ya zaka fahimta ba gaskiya ce mai matukar nauyi da daure kai, Daddy ni da Yusura ba mu taba son junanmu ba, ban taba jin ina sonta ba ita ma bata taba jin tana so na, wannan sakin ma ta dade tana bukatar na yi mata shi, saboda da nisanta da ni” Daddy yayi murmushi mai sauki ya cire gilashin idonsa. “Kareem karka maida karamin yaro mana, baka sonta bata sonka aka yi muku aure kuka zauna lafiya har kuka haihu ba a taba jin kanku ba sai yanzu da Mahaifiyarka bata raye zaka ce wai baka sonta? Wannan ba hujja ba ce” Cikin tsananin damuwa Kareem ya ce. “Wallahi Daddy bana son Yusura ita ma bata so na, kawai dai mun amsawa Momy ne kuma mun zauna saboda ita, ni da ita ba za mu iya bijirewa umarninta ba” “Okay yanzu da bata raye mu ne abokan wasarka? Kai da ita? Ni ba zan ma yarda ba ku son junanku ba. Kareem zan baka shawara karka yarda ka rasa Yusura, na yi aure tun kurciya har yanzu na zauna da mata biyu a lokacin da mahaifiyarka take raye, mu kan samu tsabani mu yi dadi, wani lokacin har iyaye su sani, amman ban taba ganin matar aure da bata taba kuka da mijinta ba sai Yusura, bata fadin sherinka, bata kawo kararka, kai a gurinka ba abun kunya ba ne aji ka saki matarka? Kuna da yara biyu me kake fada musu? Idan aure kake son karawa you're free to do so ba sai ka saki matarka ko ka wulakanta ta ba, idan har kana fadar saboda Mahaifiyarka ka aureta to miye amfanin sakin a lokacin da mahaifiyarka bata raye? Ke nan ganin idonta kake yi ma biyayya ba saboda Allah ba? Yanzu da ban yi magana ba haka zaka zuba ido ta cika idda? Ko saki uku ka yi mata? Domin bata fada mana ko saki nawa ka yi mata ba, kuma ita bata zauna kamar kai ta kalli kwayar idonmu ta fada mana bata son dan mu ba, Kareem idan ka sake ka rasa Yusura ka rasa matar kirki kenan har abada” Kareem yayi shiru be ce komai ba, domin ya fahimci Daddy ba zai yarda da duk wani zancensa ba. “Saki nawa ka yi mata?” “Daya” Sai a lokacin Daddy ya sassauta muryarsa ya daina yi ma Kareem fada. “Ka yi hakuri, shi zaman aure dan hakuri ne, duk can talkaminmu suka tsinke, dole sai an kai zuciya nesa, bana son na sake jin wata matsala a tsakaninku, ka maida matarka dakinta ku zauna lafiya dan Allah” Kareem kamar zai fasa kuka ya ce. “Daddy mai daki shi ya san inda yake masa yoyo...” Be rufe baki ba Daddy ya rufe shi da fada yana masa tsawa. “Get out Kareem, tashi ka dauki matarka ka aje ta gida sannan ka wuce aiki, wato Momy kake tsoro kana gudun zuciyarta mu kuma ka raina mu ko? Toh ka bari har bayan raina sannan ka saketa idan ka ga dama ka hada har da yayanka ka koresu gaba daya” Da sauri Kareem ya sauko daga kan kujera yana bawa Daddynsa hakuri, domin idan akwai abun da yake gudu da tsoro a rayuwarsa to fushin iyayensa ne. “Ka yi hakuri Daddy, na maida aurena saboda kai, kuma zan dauke ta mu tafi gida yanzu kamar yadda ka ce ka yafe min dan Allah” Daddy ya dauke kai ya kai hannu ya dauki gilshinsa ya mike tsaye ya shige bedroom dinsa. Kareem ya dafe kansa ya rumtse ido, ya fi karfin minti talatin a haka sannan ya dago ya fito daga bangaren ya dawo bangaren Hajiya Hassana ya zauna a falon ya kasa yin komai har sai da Step mother dinsa ta fito sannan ya gabatar mata da abun da ya maido da shi bangaren nata. “Na maida aurena Hajiya, a fada mata ta fito mu tafi” Hajiya Hassana ta yi murmushin jindadi. “Haba yanzu na ji magana, ko kai ba haka ake so, kuma dan Allah ayi ta hakuri karka ce zaka biyewa mace ita mai rauni ce, kuma duk matsala da za a samu a daina saurin saki, muna raye idan ya kamata mu ji sai ka sanar mana mu tsawatar mata yafi ayi ta saki ga yara” “Tohm Hajiya” Ya amsa irin amsawar nan na wanda ya rasa interes da mafaka da kuma gata a lokaci daya, daman tun farko yayi tsammanin haka shi ya hana shi sakinta a lokacin da Momy bata dade da barin duniya ba, da ace kuma ya sake a lokacin da take raye Allah kadai ya san irin fushin da Momy zata yi da shi. Ya mike tsaye yana jin wani fever na rufe shi ya nufi motarsa ya bude ya shiga ciki ya zauna yana jiranta bakinciki cike fal a zuciyarsa. Ya bata awa daya a haka sannan Aneesah ta fito ta bude motar ta ce masa. “Big Bro wai Hajiya tace ka tafi zata kawo ta da kanta” “Toh ki fadawa Daddy haka idan na wuce” Cikin tsananin damuwa Kareem yake maganar sannan ya ja motarsa ya fice daga gidan. Wunin ranar aiki kawai yayi dan ya zame masa dole ba dan jikinsa da zuciyarsa suna cikin dadi ba. Bayan ya gama yana kokarin hada kayansa ya wuce wata mate room ta shigo ta kawo masa takardar envelope. “Maman Khalid miye wannan” “Wallahi ban sani ba, wata ce ta zo dazun bata same ka tace bari ta ba ni na aje maka dan Allah kar na bawa kowa sai kai hand to hand” Ta fada cikin hausarta da bata gama kwarewa ba, kasancewarta bayarabiya. Ya karba fuska ba yabo ba fallasa yayi mata godiya ya hada kayan saukinsa ya fice daga office din. Sai da ya shiga motarsa sannan ya bude envelope din wani kamshi mai dadi ya bugi hancinsa, flower ce farkon abun da ya fara cirewa daga takardar sannan wani sexy chocolate da kuma farar takardar mai rubutu red. Be yi tsammanin ganin romantic abu irin wannan ba sai a Safeena kuma ya canka daidai a lokacin da ya fara karanta sakon na karin shekararsa a yau. “Happy birthday Love, barka da zagayowar ranar haihuwar mutumen da bana son zama da kowa sai shi, barka da zagayowar ranar haihuwar mai bani farinciki a zuciya da jiki, mai kwantar da min da hankali, mutumen da ke nisantarsa ke haukata ni ta hana ni sukuni, barka da karin shekara My future husband, my partner in crime, the father of my future kids, father to be... I know its your birthday today.. I am sure u will give me treat in a big house like we use to be.. so I shall talk to you in person there, because I don't know to express my feelings in paper, i love you duk yadda kake tsammanin za mu iya rabuwa da junanmu ba zamu iya ba Kareem saboda muna son junanmu, ba zan iya kyaleka a irin wannan yanayin da kake da bukatar wani a kusa da kai ba, i know how painful it's to lost a best friend and Mother. Please take good care of yourself for me...” Ya girgiza after ya gama karantawa, so today is his birthday gaba daya ma ya manta, daman tun kamin su rabu tun tana girlfriend dinsa ita take tunawa da birthday sai kuma Momy, and even after break up bata daina wishing dinsa ba a duk lokacin da ranar zata zo. Wani gurin ya bude a motarsa ya saka takardar ya rufe ya yi ma motarsa key. Kusan wannan ne karo na farko da yake jin kamar baya sha'awar komawa gidan all his thoughts is Yusura ta koma gidan by that time, hakan ne ya rike shi daga komawa da wuri domin samawa yaransa abun da za su ci da rana wani lokacin daga restaurant yake karbowa ya je musu da shi, wani sa'in kuma da kansa yake girkawa tare da su ko kuma kamin su dawo. He park his car near the entrance ya bude motar ya fito ya shiga falon. To his greatest surprised yaransa suke tarbe shi da wani irin farinciki da murna da ba su taba tarbonsa da shi ba. “Dady welcome home, Dady Mamy ta dawo” Ya rage tsawonsa yana kallonsa da murmushin da ya ara ya yaba a fuska saboda yaransa. “Kun jidadi?” “Eh sosai” Babbar ta fada sai ya shafa kanta, ba su taba tambayarsa ina Mamy su tafi ba, yaushe zata dawo me yasa bata gidan, tun da suka dawo daga school ba su same ta ba ba su sake walwala ba, kuma ba su tambaya ina take ba, kai ka ce sun fahimci sakinta aka yi, tun daga lokacin Kareem be sake kai su family house dinsa ba saboda gudun su ganta ko kuma su yi kuka idan zai dawo da su. “I'm happy too” Ya fada yana kallonsu cike da alfahari, and he's not lie farincikin yaransa farincikinsa ne, hakan kuma ba yana nufin ya jidadin dawowar Yusura ba, idan har akwai abun da yake nadama a yanzu be wuce aurenta ba, me yasa be fadawa Momynsa gaskiya from first place ko da ba zata jidadin haka ba? Yanzu a wa gari ya waya, waye a matsala sama da shi? “Kun ci abinci?” “Eh munci Mamy ta dafa mun ci, naka yana dinning Dady” “Okay bari na je na yi wanka na shirya sannan na zo na ci, ku je ku yi shirin islamiya” “Okay Dady” Karamin ya amsa, babbar kuma sai da ta sumbance shi sannan ta nufi sama da gudu tana murna. Tsaye yayi yana kallonsu har suka haye suka shige dakin Yusura sannan ya sauke ajiyar zuciya ya haura stairs din ya shiga dakinsa. Bayan yayi wanka ya kwanta a dakin yayi bachi awa daya ya farka, bandakin ya shiga yayi alwala ya fito ya saka ya sauya tufafin jikinsa daga kanana zuwa shadda sannan nufi madubi ya dauki dan'uwansa turare ta feshe jikinsa sannan ya dauki wayarsa ya wallet dinsa then car keys ya fice daga gidan gaba daya. A hanya ya tsaya yayu sallah la'asar sannan ya karasa restaurant dinsa. Yana shigowa reception din Nabil da ya gama dutysa zai fita ya gaishe shi cike da girmamawa. Kareem ya mika masa hannu suka gaisa. “Ka gama naka eh?” “Eh na gama ranka ya dade, daman duty safe nake yau, ko akwai abun da zan yi?” “No aa, ka ce ka daina karatu?” Ya gosa kansa cikin jin kunya ya amsa domin abun kunya ne wannan zamanin a kalli matashi kamar shi ace baya karatu a . “Eh Wallahi, amman dai zan koma nan gaba idan Allah ya yarda” “Me ka taba karanta? Wane course?” “Mass Com na fara, amman dai ina son nan gaba idan zan koma na canja course” Kareem ya cigaba da tafiya yana fadin. “Why baka son aikin jarida ne?” “Ina son, amman dai yanzu na fi sha'awar Public health” “Karatun health yanzu yayi yawa, why not ka yi political science? Karatun yana da kyau, kuma idan ka dace da gurin aiki kamin an ankaro ka dauke nauyin gidanku” “To da har ka kawo wannan shawarar da yardar Allah shi zan yi ranka ya dade” Kareem yayi murmushi yana jindadin yadda Nabill yake girmamashi. “Na jidadin haka, ni kuma zan yi kokarin sama maka scholarship, a private ko kuma gov school, ban sani ba ko a samu a nan gida nigeria ko kuma a waje, fatan dai ba zaka ba ni kunya ba” Nabil ya rasa me zai ce ya rika hannun Kareem yana son masa godiya ya kasa domin be taba kawo wani zai dauki nauyin karatunsa ba, wanin ma kuma Kareem. “Ranka ya dade, na rasa me zan ce ma” “Toh ka aje kalamanka sai idan an samu tukuna, sai ka yi godiya” Cewar Kareem yana dafa kafadarsa sannan ya wuce yana murmushi ya bar Nabil tsaye da mamaki. Be yi taku goma ba ya juyo ya kalli Nabil. “Nabil ya Noor take?” Nabil ya hade yawun bakinsa da sauri ya matsa yana amsawa. “Ta.. Tana lafiya ranka ya dade” “Ba wata damuwa babu wata matsala?” “Eh to tana dai cikin damuwa, mutuwarta nan ta dan taba ta gaskiya, domin ta canja gaba daya kamar ba ita ba” Kareem be ce komai ba, ya juya ya cigaba da tafiyarsa. Office dinsa ya shiga sai da ya zauna sai kuma ya tashi yake yi yanzu a duk lokacin da ya shigo, da zarar ya kalli kujerar da Hafiz yake zama idan ya shigo office din da yamma sai ya ji babu dadi. Har yanzu ya gagara sabawa da rashin abokinsa wannan kawa zucin yana nan tare da shi, shi ke hana shi walwala a duk lokacin da ya shigo office din. Be wuce minti ashirin a ciki ba, ya mike tsaye ya dauki keys dinsa ya fice da kansa ya shiga ya saka aka zuba masa abincin da yake sha'awar ci yaron gurin ya rika masa har gurin motarsa. Front seat ya bude aka zuba abinci sannan ya rufe ya shiga bangaren tuki yaja motar ya fice daga restaurant din gaba daya. Tuki yake not knowing what to do or to go, shi dai gashi nan duniyar gaba daya ta ki ta yi masa dadi. Be faka ba sai da ya samu wasu itatuwa dake gefen hanya, ta cikin itatuwan ya ratsa ya faka motarsa sannan ya bude ya dauki abinci yana ci, gurin is so fresh ga wani iska mai dadi babu damuwa ko hayaniyar kowa it's just him and himself. NOOR POV A kwana a tashi babu wuya ga Allah, kamar jiya na fara wanka duk dai wasu sukance wankan be wajaba a kaina ba, saboda ya sake ni, sai dai zancen da ya fi karfi shi ne na yin zaman takaba domin akwai gyara a auren kuma ban kai ga cika idda ba ne ya rasu. A ranar da na yi wata hudu da kwana goma Mama ta aiko da waina da fanke aka raba sadaka yan'uwanta suka zo tare da yan'uwan Baba aka saka ni na yi wanka na saka sabuwar atamfar, a ranar kuma mutuwar Hafiz ta dawo min sabuwa kai kace mun yi shekara aru aru da shi ba yan watanni ba, sai dai abun da ya daure min kai shi ne na rashin zuwan dangi ko yan'uwansa a gurin tun a ranar da na dawo gida har zuwa yau babu wanda ya leko ni ko ya bincika lafiyata, abincin da ake cewa dangin miji ma suna kawowa matarsa idan tana takama basu kawo min ba. Wata kila Aisha ta shafa min bakin fenti a idonsu domin na lura har bayan mutuwar Hafiz kishi take da ni. Bayan sallah Isha'i, a lokacin da kowa ya watse, ina zaune ina gyara wake soya Yaya ya shigo cikin gidan da kuzarinsa ya ce. “Noor oga Kareem ne a waje yace na kira ki” Na yi shiru na wasu dakiku sannan na mike tsaye kamin na cira kafa na ji Umma ta tabe baki tana fadin. “Wannan ai ba mutunci ba ne, ace ana maka sallama ka mike kai tsaye ka fice ba tare da tunanin fadawa mahaifi ba, kai ma ai ba ita ya kamata ka samu kai tsaye ka fada mata ba mahaifinku ya kamata ka fadawa” “Ba kisan waye oga Kareem ba Umma, oganmu ne na gurin aiki kuma abokin mijinta nw Hafiz ya saba zuwa nan akai akai” Ya Nabil ya bata amsa. “Tohm Allah ya kyauta, tashi ki tafi, amman gaskiya idan haka mahaifiyarku ta koya muku ba abun kirki ba ne, ai sai uba ya aminta ake fita domin shi yake aurar da yarinya” A kam ban iya rike kaina ba sai da na mayar mata da martani. “Baki san komai akan uwarmu ba, karki sake fadin wata mummunar kalma akanta” Kallona ta yi ta dauke kai bata ce komai ba, ta cigaba da dakan yajin da take. Ni kuma na shiga ciki na dauko hijab dina na saka na fito kofar gidanmu. Sai na same shi a gurin da suka saba tsayuwa shi da Hafiz idan sun zo, ko kuma idan ya zo shi kadai. Ganinsa ya tuna min da Hafiz sosai sai zuciyata ta yi min babu dadi, shi kuma na lura baya cikin walwala da farinciki, gashi ya rame kamar ni yayi hudu haskensa ya rage. Gambun motar dake bude ya rufe sannan ya jingina da motar yana kallona kamar wanda be taba gani na ba. “Noor how are you now?” Tambayar yake ya nake, amman sai na ji kamar yace na fada masa damuwata ta hanyar kukana. Kawai sai na fara hawaye ina kallonsa, i miss him i miss his friend i miss my previous life. “Kina cikin damuwa ko?” Na daga mishi kai, sai na ji ya sauke ajiyar zuciya. “Duk yadda kike tsammanin abun ya wuce nan Noor, na fi ki shiga damuwa yanzu, i loss hope, kawai ina rayuwa da kokarin tsayawa saboda Yayana, a yanzu babu wani daki da zan iya rufe kaina na ji sanyi, duka dakunan zafi ne da su kamar wuta” Na share hawayena. “Da zan iya komawa na gyara rayuwata ta a baya...” Na ji ya fada sai kuma yayi shiru be cigaba ba. Ni kuma na kalleshi na ce. “Da ka goge shafina a rayuwarka” Ya girgiza min kai. “Ba zan iya goge ki a rayuwata ba Noor ko da kuwa ace ina da wannan damar, ba ki min komai ba, babu dalilin da zai saka na natsane ki, you're just innocent, precious soul, and Hafiz was right akan abubuwa da yawa akanki” “toh me zaka gyara?” Yayi murmushi ya gyara tsayuwarsa. “Ba wannan ya kawo ni, na zo nan ne saboda na yi magana da ke da kuma Baba, amman kamin nan fada min ya kike?” “Ina lafiya, amman mutuwa bata da dadi Kareem, shiyasa lokacin da Hafiz ya fada min mahaifiyarka ta rasu, na yi kuka sosai na tausaya maka yanzu kuma na ji yadda ake ji” Murmushi yayi ya daga kansa sama sai kuma ya sake kallona. “Noor... Kamin na manta, na zo nan ne saboda maganar gadonki da kuma kayan dakinki” Na cigaba da kallonsa ina sauraren abun da yake fada. “Noor dan Allah karki ce zaki yi jayayya da iyayen Hafiz akan gado ko wani abu, sun ce baki da gado kanensa ya kira ya fada min kuma na je na same su na yi musu magana na fahimtar da su, amman ba su yarda ba, iyakar hujjarsu wai Hafiz ya sake ki kamin ya rasu, kuma kamin ya sake ki wai be taba tarayya dake ba haka ne?” A nan na sauke kaina kasa na dan bata rai. “Aisha ta bata ni a gurin kowa, kuma ita ce silar duk faruwar haka” “Babu wanda zai iya bata ki a gurina, kuma mutuwar aure abu ne da Allah ya kaddara, kuma ba dan Allah ya rubuta haka ba, na yi magana da Hafiz kuma yayi alkawarin yana dawowa zai zo ya dauke ki ku tafi gidan tare, sai dai kamin ya iso Allah yayi ikonsa” “Da gaske?” Ya daga min kai. “Yes Noor na lura kina cikin damuwa a lokacin kuma kin fada min kina son komawa ai, babu wani abun da zaki roka ban miki shi ba Noor sai idan ba zan iya ba” “Na dauka ina takura maka ne, na ga har baka son zuwana gurinka, na san ni ina da takura ai” Yayi murmushi. “To ki yi hakuri, idan Baba yana ciki shiga ki masa magana” “Baya nan yana majalisa” “Shiga ciki zan je can na same shi, ki kwantar da hankalinki Allah zai baki abun da ba su ba ki ba, kayan dakin ma sun ce ba za su baki ba ai saboda shi yayi komai” “Ni fa ba abun da ya dame ni da wani gado, su je su yi ta riko, amman ka yi magana da Baba shi ne dai na ji yana zancen zai yi kara idan ba a bada ba” “Okay” Kallona yake har na shige cikin gidan, ina shigowa Ya Nabil ya fita waje.Duk wata maganar da zai yi da Baba na san ba zai saurare shi, amman kudi za su iya sakawa ya fahimci komai kuma ya sassauto. Da alaka kuma Kareem yayi amfani da su ne domin babu ya shigo da far'a har da tsarabar nama yayi ma Umma. Cewa yake a yanzu ya hakura zai kyalesu amman saboda Kareem be kawai ba dan haka ba da babu abun da zai hana shi jan min hakkina. Yanka biyu aka ba mu, sai da muka cinye sannan yayi mana albishir wai Kareem ya fada masa ya nemawa Ya Nabil karanta a Sudan. Farinciki ya cika ni a lokacin da Baba yake fada min Kareem yana neman izininsa idan ya aminta sai ya fadawa Ya Nabil din ya kai masa takardunsa na SSCE. Sanin da na yi ba karamin dadi Ya Nabil zai ji ba, ya saka ni farincikin da na kwana biyu ban yi ba. Hakan kuma ya karantar da ni cewar Kareem yana da kirki ta wani bangaren, domin gashi ya danne kudirin mahaifina kuma yana kokarin nemawa dan'uwana karatu alhalin be hada komai da mu ba. Farinciki a gurin Yaya Nabil ba a magana kamar zai zuba ruwa kasa ya sha domin murna, daman abun da yake nema ne yana son karatu shi da Hana ba kamar ni ba. Washe gari da safe Kanen Hafiz ya sake kawo min ziyara sai dai wannan karon ba, maganar gado ce ta kawo shi ba, ya zo min ne da tsaraba ta atamfa biyu da kuma turare sai sabulu da talkami da kudi 10k wai yana taya ni murna fita waka, kuma na yi hakuri da yadda yan'uwansa suka nuna min halin ko'ina kula. Na karba na yi masa godiya muka yi sallama na shiga ciki, bana tunanin ina da wata bukata ta kudi a yanzu wannan ya saka na dauki kudin na bawa Hana na ce ta kaiwa Mama idan ta tafi gidan, domin ita ce mai yawan zuwa ni ban taba zuwa ba domin an yi auren ne a lokacin da ba ni da halin yawo. Abu kamar wasa, shiryen shiryen tafiyar Yaya Nabil Sudan ya fara, duk wani abu da za'ayi Kareem ne yake ba shi kudi yayi, har aka kammala komai within three months. Ranar da zai je yi ma Mama bankwana na bi shi muka tafi tare, ni da shi sai a ranar muka fara zuwa gidan. Babba gida ne mai bangare kusan hudu, gida ne mai kyau da tsari Mama da kanta na san ba ta taba mafarkin aure irin wannan gidan ba. Da muka shiga ciki sai ta zame mana kamar wata bakuwarmu saboda yadda rayuwa ta canja mata, ta yi kiba ta kara haske ga tufafi masu tsada kayan kallo kai har da dinning da ac kamar daman can Mama bata taba auren talaka ba, duk inda ta wulga kallonta nake kamar wata bakauya. “Noor na zame miki sabuwa yanzu ko?” Na yi dariya ina kallon plate din taliyar da ta aje min nama batsa batsa kamar wanke. “Mama ina ta mamaki ne, ina kika hadu da wannan mutumen ne?” Ta dan hade rai. “Mutume? Toh idan ba zaki iya kiransa da Baba ba, ki kirashi da suna Alhaji kamar yadda kowa yake kiransa a gidan nan, wato ke dai sakarcin ki ba zai canja ba ko?” Na yi shiru ina kallon Yaya dake cin taliyar, sannan na soma cin tawa. Rabin abincin kawai Yaya ya ci ya sha ruwa yace zai tafi. “Da wuri Nabil na yi zaton sai dare, saboda Alhaji ya dawo ku gaisa, yana ta fadar ban taba gabatar masa da sauran yarana ba, be san kowa a cikinku ba sai Hana da ke yawana zuwa” “Bana son na kai dare Mama, akwai guraren da ya kamata na tafi kamin ba bar garin nan, kuma kin ga kwana biyu ya rage min” “To sai dai kai ka tafi Noor kuma zata tsaya sai ya dawo kun gaisa tukuna ta wuce” Mama ta shiga dakinta ta dauko masa babbar leda cike da kaya sannan ta danka masa 20k tana ta sakawa Kareem albarka wai daman a yanzu tana ta tunanin wace makaranta zata nemawa tarin kudin da take shi take yi ma, amman gashi ya dauke mata nauyi. Bayan Ya Nabil ya wuce muka zauna da Mama muna hira take tambaya ko Zafeer ya ji rayuwar Mijina. “Zai iya ji tun da iyayensa suna cikin unguwar, ko basa nan ma ai yan gulma suna nan, fitowar nan ma cewa suke ta yi hakkinsa ne” “Zafeer yana sonki sosai, zai iya dawowa yanzu ma, wata kila kuma iyayensa su hana shi, ko da yake a can baya ma sun yi ta kokarin hana amman ya nace sai ke, gashi kuma an watsa masa a ido, Wallahi mahaifinku be kyauta ba” “Baba ma da yace be yafe ba idan na sake masa magana, shi ne abun da ya fi damuna” “Wai har yanzu? Toh ai Hafiz din baya raye kuma, yanzu idan Zafeer ya dawo ba zai bari ya aureki ba?” “Ban sani ba, amman da kamar wahala saboda yana ganin Zafeer talaka ne” “Haka ne, ubanki be ji wani yare sai na kudi, gashi babu mai iya ja masa liyi a dangi komai yayi daidai ne a idonsu” Na daga kai ina kallon POP din falon. “Taso mu tafi ki gaisa da mutanen gidan, suna ta tambayar, da kika fita wanka ma sai da matarsa tace zata tafi ta duba ki kuma Allah be yi ba” “Ita bata kishi ne Mama?” “Ana tabawa mana ayi mace babu kishi, amman boyewa ake na ciki na ciki, ita dai tana da kirki ba kamar wasu ba” “Ko dai irin na Aisha take miki ba, haka take nuna min ba komai ashe wayo take min” “Ke dai da halinki Noor, na san ki ba, kuma zamanmu a nan Alhaji ya fada mace kamar riga take a wuyansa duk wanda ta daga masa hankali cire ta kawai zai yi ya aje, duk tarin yaransa babu wanda uwarsu take cikin gidan nan, sai wannan matar da yaranta uku, sauran duk iyayensu sun fita, ni ma sai bayan auren nake ji, wata kila shiyasa ta kama kanta” Ina jin haka na san an gudu ba a tsira ba ne, kenan ita ma idan ta yi masa ba daidai ba zai iya sakinta. Daga bangaren Mama muka fito muka shiga bangaren matar da take gidan a yanzu. A cike muka samu falon da mata da maza, Mama ta yi sallama suka amsa suna gaisheta da mutunci. “Noor Ya hakuri?” Wata budurwar da ban waye ta ba ta fada sai na amsa da Alhamdullahi na gaishe da Hajiyar. “Lafiya Kalau Noor, an fita wanka ko? Tohm Allah ya bada hakuri ya kawo na gari” Mama ta amsa da Ameen. “Alhaji ne be santa ba sai mita yake ina boye masa yara, tare da yayanta take jibi zai wuce Sudan gurin karatu, ya zo bankwana amman be tsaya ba, ita kuma ba ce ya tsaya ta gaisa da yan gida” “Ta kyauta gaskiya, da ma dai kin maido nan kila zata fi jin sanyi kin san gidan na mu cike yake da mutane” “Mahaifinta ne ai be yarda ba, ko takaba a nan ya so ta yi amman uban yace ba zata yi ba” “Kin san wasu mazan akwai kishi” Haka dai suke ta hirarsu ni dai kaina na kasa ban dago har sai da na ji an bude kofar falo alamar mutum ya shigo. Dagowar da na yi sai muka yi ido hudu da Safeena tana dauke da cikinta da be gama girma ba. Bata kallon kowa sai ni ni ma kuma bana kallon kowa sai ita muka rika kallon kallo wata kila ita ma tana mamakin ganina ne kamar yadda nake mamakin ganinta. Gidansu ne? Ko kuma zuwa ta yi? Ko kuma dai tana da wata alaka ce da mutanen gidan? “Kin dawo Safeena?” Hajiyar ta fada sai Safeena ta amsa mata ba tare da ta kalleni ba, har lokacin ni take kallo. “Na dawo Hajiya, na karbo files din gobe zan tafi asibitin na kai” “Toh Allah ya taimaka ya raba lafiya” “Ameen” Ta amsa sannan ta dauke idonta ta zauna a kujerar dake facing dina, sai kuma ta sake dasawa daga inda ta tsaya. “Anty Safeena kin santa ne?” Na kalli mai tambayar wata kila su ma sun lura da kallon da take min yayi yawa. Ga mamakina sai ta amsa da cewar “Aa ban san ta ba, wacece hala? Ta yi min kama da wata kawata ce ta yarinya” “Noor ce yar wajen Anty Amarya, wanda mijinta ya rasu” “Allah sarki Allah ya masa rahama” Ya juya tana kallon Mama dake amsawa da Ameen sannan ta sake kallona. Har muka baro bangaren babu abun da take sai kallona kamar wata bakuwarta. Ban kuma san dalilinta na boye cewar ta san ni ba. A bangaren Mama na koma na zauna har dare ina jiran dawowar mijinta saboda mu gaisa, be shigo ba sai bayan Magariba a lokacin da ake hada hadar Sallah Isha'i. Na yi mamakin yadda yayi murna da farinciki ganina babu wata kyama, har na na yi sha'awar ina ma ace shi ne mahaifina ba Baba ba, zaunawa yayi a falon yana ta min nasiha akan hakuri da rayuwa na halin da na samu kaina da kananan shekaru, na yi masa godiya ya saka hannunsa aljihu ya ciro 10k ya ba ni. “Aa na gode” A bakin gaskiya ta ba zan karba ba, domin ko na karba ban san miye zan yi da su ba a yanzu. Sai dai na lura hakan be masa dadi ba domin rufe ni yayi da fada a dole na karba na yi masa godiya. “Tafi bangaren Hajiya ki ce na ce cikin yaran nan duk wanda yake nan ya sauke ki gida” “Tohm” Na mike tsaye na yi ma Mama sallama sannan na fice daga falon yana ta kallona. Bangaren Hajiyar na dawo na sanar mata abun da Alhaji ya fada sai mutumen dake tsaye a gabanta yayinda take zaune ya juyo ya kalleni. A nan ma wani mamakin ya kara kama ni, mutumen nan da ya taba yunkurin biya min kudin siyayyar da na yi a wani dare da muka fita tare da Hafiz. “Kamar na sanki?” Na bude baki kamar zan yi magana sai kuma na yi shiru, ban san me zan ce ba, ni dai ina da saurin gane mutane shiyasa na gane shi. “Noor ce Yar wajen Anty Amarya ce, ita ce wadda mijinta ya rasu” “Ai ban sani ba, Allah ya jikanshi da Rahama” “Ameen, ku tafi tare sai ka sauke ta ka wuce, Noor bari ga Abdull zai fita yanzu sai sai ya wuce da ke, ki jira shi a waje” “Okay” Na juya na fito daga ciki, ban san wacece motarsa a cikin motocin gidan ba dan haka zauna a balcony har ya fito. “Kika zauna a kasa?” Bance komai na na mike tsaye na bi bayansa muka isa gurin wata sabuwar mota, sai da ya fara shiga sannan na bude na shiga front seat. Ba tare da yace min komai ba yayi reverse ya fice daga gidan. “Ina ne unguwarku?” A lokacin da na dago sai na ga idonsa akaina suke. Na fada masa na sake maida kaina kasa kamar ba ni ba. Na ji lokacin da wayarsa ta yi kara ya amsa. “Hello Safeena...” Sai kuma yayi shiru, yana sauraren abun da ake fada masa. “Yanzu na fito gida, amman zan biya ta can, sai na zo miki da shi, shi kadai kike so ko da wani abun?” Na yi shiru ina saurarensa kamar wata Munafuka kamin na ji ya ce. “Okay sai na dawo” Ya aje wayar ya dago zan kalleshi idona suka fada cikin nasa da sauri na dauke kaina ina jin sautin murmushinsa. Ban sake kallon gefen da yake ba har muka isa unguwar. “Ka sauke ni a nan unguwar bata da kyau can ciki” Na fada. “Karki damu, amanarki aka ba ni sai na kai ki har gida” Yadda ya fada haka ya aiwatar har kofar gidanmu ya isa da motarsa ya faka, ni kuma na bude na fito zan rufe kofar ya ce. “Ba godiya” Ban ce masa komai ba na rufe motar, na gode masa sai ka ce rokonsa na yi ya kawo ni. Sai da na shiga gida sannan na ji motarsa ta bar kofar gidan. KAREEM POV. Yana gama sallah asuba ya shiga kitchen hadawa yaransa breakfast. Domin Yusura bata musu komai tun da ta dawo gidan, Kullum shi zai hada musu breakfast ko kuma ya saka aika musu daga restaurant dinsa kamin su tashi break. And now cooking is one of his favorite things, yana samun nishadi a girkin, musamman idan yaran suka farka suka same shi a kitchen suna hayani yana aikinsa har ya gama, ya karya tare da su wani sa'in kuma ya zuba musu na su, ya tafi da nasa a office ko kuma su su tafi da na su school shi kuma ya ci a gida. Idan ya fita sannan Yusura take saukowa ta gyara ko'ina ta dora na rana. Tun da ta dawo gidan be taba leka dakinta ba, be taba ce mata uffan ba, ita ma kuma bata bari sun hadu ba, da zarar ta ji motarsa ko ta san lokacin dawowarsa sai ta shige dakinta. Yau ma sai da ya raka su har gurin bus sannan ya dawo ya zauna ya ci nasa breakfast. Bayan ya gama ya mike tsaye ya shiga dakinsa yayi wanka ya shirya cikin kananan kaya ya fito yana rike da lab coat dinsa da wayarsa sai kamshi yake zuba. Yayi kyau sosai ramar da yayi ta kara masa kwarjini da haifa. Sai da ya fice daga falon sannan Yusura ta sauko a zatonta ya fice gaba daya, dinning ta nufa ta tsaya tana kallon kayan karyawar da ya shirya, biredin da ya gasa ta dauka taba tabe baki ta shinshina ta aje. Sannan ta ja kujera ta zauna ta bude flask din ruwa zafi, a daidai lokacin Kareem ya turo kofar falon ya shigo domin daukar wallet dinsa da ya manta a dakinsa. Kallo daya yayi ma gurin da take zaune ya dauke kai ya haura sama ya dauko wallet dinsa ya sake fice. Yusura bata taba jin kunya irin ranar ba, bayan amincewa da aurensa da ta yi wannan ne abu da na biyu da take bakinciki a rayuwarta, ji ta yi kamar ta fasa komai na gidan dan bakinciki. Tuki yake a hankali har ya isa asibitin, ya faka motarsa a gurin da aka rubuta Dr Kareem sannan ya fito ya dauki kayansa ya rufe motar ya shiga cikin Babbar asibiti ana miko masa gaisuwa yana amsawa. Office dinsa ya shiga ya fara duba takardun dake gurin sannan ya fita ya fara duba marar lafiyar da aka aje da ya kamata ya duba su. After ya gama ya dawo ya zauna a office dinsa patient din dake shigowa suka fara shigowa yana dubata. Third person da ta shigo ita ce Safeena, tana sanye da dogon Hijabinta har kasa sai dai hakan be boye cikin dake jikinta, har ta zauna ita yake kallo. Sai da ta aje jakar dake hannunta sannan ya jingina baya ya kwanta jikin kujerar yana kallonta. “Wai ke wace irin yarinya ce Safeena?” “Ni din wata yarinya ce, mai wuyar warke ciwo, wata yarinya ce da ka koyawa soyayyarka kuma kake kokarin guduwa bayan ka yaudareta da farko” “Gargadin da na yi miki, da kuma tazarar da na baki daga lokacin da muka yi haduwar karshe zuwa yau bata fahimtar dake, na rumgumi kaddarata, ke ma ki rumgumi taki?” “Ka rumgume kaddara saboda Yusura tana sonka tana kyautata maka a yanzu? Ko kuma daman can karya ka yi min kace bata kula saboda kullum ka rika samun biyan bukatarka da ni? Ka yi breaking heart dina da farko yanzu kuma bayan na saba mu'alama da kai na saba da kwanciya a kirjinka na saba da soyayyar kake tunanin sake guduwa ka bar ni?” Ya mike tsaye daga zaunen da yake ya nufi windows dinsa ya bata baya. “Kana da kyau, Kareem kana da kudi amman duk wannan be tabbatar min da ina sonka ba sai da mu'amala ta hada mu, all this while na kyale ka ne saboda ina dauke da cikin nan” “Me kika zo yi yanzu? Tashi ki fice daga office din nan” “Baka da wannan damar ba saboda da kai na zo ba, saboda cikin nan ne, na dawo da awon cikin nan a nan ne, a nan zan yi ta zuwa har zuwa lokacin da zan haihu” Ya dafa Window ya rike kansa. “Namiji zan haifa suka ce, kuma ina alfahari da haka” Kareem ya dauki lokaci a haka kamin wani tunanin ya zo masa sai ya juyo da sauri ya kalli cikin na ta sannan ya kalli fuskarta, sai ta yi masa murmushi. “Fita ki bar office din nan” Ya nuna mata kofar, zata sake magana da daka mata tsawa har sai da ta zabura. “Fita ki bar office din nan na ce” Ta mike tsaye da sauri ta dauki jakarta tana kallon yadda ya hade fuska kamar be taba ganinta ba, ta fice daga Office din. Dawowar yayi ya zauna kan kujerar ya dafe kansa ya runtse ido yana numfashi da karfi, ya girgiza kai kamin ya daga hannunsa ya buga a tebur din yana jin wani irin bakinciki marar misaltuwa... It could be a joke maybe tana gwada shi ne, if not ai tana da hankali matukar ba wata manufa take da ita akansa ba ba zata taba sha'awar haihuwa da shi alhalin tana da aure ba, ta dauki dawainiyar cikin da ba na mijinta ba ta kai masa yayi komai, ba zata fara ba. Abun da zuciyarsa ta raya masa kenan har ya ji ya samu saussaucin cigaba da aikin da yake. Sai da lokacin tashi aikinsa yayi ya tuna da ba shi da abokin hira ko shawara a yanzu domin Hafiz is no more balle ya fada masa hasashensa ko damuwarsa.Baba yana kallona ne kamar ni na kashe Hafiz saboda, Hafiz ya tafi be samu kyautatawa Baba kamar gyara masa gida ko kuma yi masa wata babbar kyauta da yake tsammani ba tun a bayan aurena. Ni ma ban fahimci hakan ba sai a ranar da Hafiz ya cika sati daya da barin duniya, Mama ta kira waya tana kara kwantar min da hankali, bayan mun gama wayar ne Baba ya rufe ni da fada wai na ci amanarsa wata kila da na kyautata masa da yanzu Allah kadai ya san yadda rayuwa zata zame mana. “Daman sai da zuciyata ta raya min ba zaman lafiya kike da yaron nan ba, saboda juya min baya da yayi ko lokacin da gobarar nan ta tashi be zo yayi min jaje ba, be ba ni komai ba, ashe ma ba zai dade duniyar ba, kina ta shuka masa rashin mutunci, in ba shi ba taya za su ce wai ba za ki masa wanka ba? Ta ina aka taba haka so suke su hana miki gadonsa kenan” Ni dai bance komai ba, gaba daya duniyar bata min dadi, ni kaina ina dorawa kaina nauyin da ba zai gogu ba saboda hana mijina hakkinsa da na yi, ya tafi da abun a ransa kuma na daukarwa kaina zunubi. “Wallahi zan iya kararsu akan haka, domin babu hujjar da tace ba za a baki gado ba, na bincike limin yace kina da hakkin wanka domin an riga da an daura muku aure, kuma sakin da yayi miki ai ba ki cika idda ba” Sai a lokacin na kalleshi cikin wani irin rauni da damuwa na ce. “Baba dan Allah ko da sun ce ba za su ba ni hakkin wanka ba, dan girman Allah dan Isar Annabi, Baba kar kace zaka yi kara ko fada ko kuma daukar wani mataki, dan Allah ka kyale su, idan ma ina da hakki Allah ya sani zai saka min” “Toh haka za a zuba musu ido su ci su cinye hakkinki Noor? Idan aka karba ai ko wani abun a rage da shi, dubi yadda gidan nan yake fa, ko gyara aka yi ba a rage ba? Allah kadai ya san abun da bawan Allah nan ya bari” “Ko ma dai miye bari Baba mai karewa ne, rayuwar ma ta kare balle kuma abun da rayuwarta ta aje, ni dai da zaka yarda da magana ta Baba da ka yi hakuri ka kyale komai dan Allah” “Ai daman ke sakarya ce baki san komai ba, sai shashanshanci, ba dan kin nuna masa rashin tarbiya da rashin hankali ba yaushe zai sake ki? Allah ya wadarranki Noor, duk yadda nake ganin kamar zaki natsu ko ki yi hankali ba zaki taba yi ba, duk yadda bake ganin kamar sanadinki wata kila zan warke sai kin kunyartar da ni, ke dai har abada va yar arziki ba ce” Ya rufe da fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba. Ni dai kam na san ban yi dacen abubuwa da yawa ba a rayuwa ciki har da uba. Domin ko a labari ban taba jin uba makamancin nawa ba, mai tsananin kwadayi da son abun duniya. Na sani sarai idan na kara wata maganar zai iya rufe ni da duka, a dole na yi shiru na ina ta sauraren masifarsa har yayi ya gama ya fice daga gidan. Haka na gagara tashi a gurin har Hana ta dawo daga makaranta ta same ni zaune a kofar dakin, ni ba kuka nake ba damuwa karara a fuskata, tunanin yadda rayuwa zata zame min nake, hankali ko tunanin da suke ganin kamar ba ni da shi ina da shi, ni na san ina da shi, idan ma babu a da to yanzu yana tare da ni. Rayuwar gidance nake jin kamar ba zata min dadin zama ba, gashi kuma ba ni da wani gurin rabawa da zan zauna na ji sanyi. Yunkurawa na yi na tashi na nufi gurin da kayan wanke wankemu suke na wanke komai tass Hana kuma ta dora girki ta girka mana shimkafa da miya, duk da kasancewa white rice and stew are my favorite amman ban iya cin wani abun kirki ba, daman abinci ya daina burge ni. Kamar wani zanenen al'amari a daren da muka yi haka da Baba sai ga kanen margayi ya zo gidanmu, ban san ya aka yi ya gane gidan ba, kusan ni dai zan iya cewa ban taba ganinsa ba, idan ma na ganshi ba zan iya shaidar fuskarsa ba, domin ban jima a gidan ba balle na san duka yan'uwansa balle kuma mazan da be gabatar min da su ba. A zauren gidanmu ya shigo bayan yayi sallama Hana ta yi masa izinin shigowa. Dogon hijab ne a jikina har kasa kaina kuma a kasa na kasa kallonsa ganin nake kowa kallona yake a wani muhalli da Aisha ta saka ni a idonsu. Bayan mun gaisa ya gyara tsayuwarsa ya ce. “Ya Hakuri Noor?” “Alhamdullahi” “Haka Allah ya so sai hakuri, shi kuma Allah yayi masa rahama” “Ameen” Na amsa ina jin idanuwa suna cika da kwalla. “Na san babu dadi, musamman ma ke da kike farkon shiga gidansa ba ki jima ba mutuwa ta yi muku gaggawa, amman duk da haka ki yi hakuri yana cikin jarabawa ne” “Haka ne, na gode” “Na san ba ki san ni sosai ba, ni kane ne a gurin Margayi uwa daya uba daya, ni ne kanensa na biyu, makasodin zuwa na a nan shi ne... Abubuwa marasa dadi sun shiga kuma za su biyo baya na sani, amman dan Allah ina son ku kawar da kanku musamman ma ke, ki yi hakuri da abubuwan da zaki ji ko ki gani” Na yi shiru ina ta sauraren bayaninsa da ban fahimci inda ya dosa ba. “Na ji wasu abubuwan ne da ba su min dadi a gidanmu, na iya yadda zan iya na taushe abun amman ya gagara saboda haihuwarmu aka yi ba mu muka haife su ba, dole sai hakuri, amman na san ke zan iya neman alfarma a gurinki kuma na roke ki duk kuwa da ba ki san ni ba, amman ina rokon alfarmar dan Allah karki ce zaki yi jayayya da iyayen margayi akan gadonki, ke ba da kike da shi ba balle ace saboda da gaba, kina gama wanka na san In Shaa Allahu zaki yi aurenki, bana son na ji wata matsala ta taso daga gurinki, ni dai ina kyautata miki zato sosai” “Ni ba zan iya jayaya akan abun da rai ya tara kuma ya tafi ya bari ba, wanda ya tara abun ma ina yake? Toh me zai saka ni yin jayayya? Idan ma ina da hakki abun da za su ba ni ba zai taka kara ya karya ba, ba shi ne gabana ba, kuma na maka alkawari ba zaka taba jin wani abu makamancin wannan daga bangarena ba” Ya sauke ajiyar zuciya yana kallona. “Na yi farinciki da jin haka, na jidadi sosai Allah ya saka miki da alheri, ya baki wanda zai maye miki gurbin Ya Hafiz har ma ya fi shi” Na yi shiru ban iya amsawa da Ameen ba. Daga haka yayi min sallama ya tafi, ni kuma na dawo cikin gidan ina ta mamaki mi ya ji danginsa ana fada har dauko kafafuwansa ya zo ya tari nawa fadan, ni kan idan gado ne ko nawa ne ba zai daga min hankali ba balle ya saka ni yin magana ko daukar wata dokar tsorona duk na Baba ne. Ban fadawa Baba wani ya zo ba, sai dai na lura hakan be yanke komai daga hanzarinsa na niyar saka iyayen Hafiz a kotu ba, idan har ba su ba da hakkina na wanka ba, na fahinci hakan ne ta dalilin wayar da na ji yana yi da yayansa wai ya bincika ko'ina ance ina da gado, dan haka ba zai saka musu ido su cinye min hakkin ba. Ban ce komai ba daman kuma ban isa na ce ya rufe da fada ba mamaki ma ya kara min duka. Zaman gidan sam baya min dadi kamar ina zaune a kaya haka nake ji. Ba ka kamar lokacin da sabuwar matar da Baba ya aura ta tare a gidan. Gaba daya sai gidan ya kara fice min a rai, domin na lura ta shigo da wani salo na hana mu walwala ni da Hana da kuma Yaya, gara ma yaya ba a gidan yake wuni ba, sai dare yake dawowa ni da Hana ne muke ganin rayuwa a gidan. Babu kuma wanda ya isa yayi magana domin mun san halin Baba ba zai taba yarda da mu ba. Umma bata wuce wata biyu ba a gidan ta cigaba da sana'o'inta da take, daman na ji Hana na fadar wai ance tana siyar da kunun waken soya kuma tana wara tana kosai, domin ba yar garin Kano ba ce asalinta yar riɓa ce dake can kusa da zuru ta birnin kebbi amman take zaune a nan Kano gurin Yayarta bayan rasuwar mijinta na farko, tana sana'a har Allah ya kawo mata Baba ya aureta a yanzu. Bata taba haihuwa ba a wacan auren nata kamar yadda take labarta masa wani lokaci ni da hana, ba wata babbar mace ce be domin Mama ta yi kanwa da ita ta biyu, sai dai tana da irin jikin nan sosai da zata iya daukar Mama da irinta uku ta goya ta gudu, domin ni da Mama jikinmu daya, ita ba kiba ni ma babu kibar, ba mamaki ma kibar ce ta burge Baba ya aurota. Wani sabon salo da ta kirkira shi ne na dorawa Hana tallar awarar a titi tana siyar mata kullum zata bata 500 naira, ita kuma tana yin kunun waken soyar a gida, ana shigowa ana siya sai dai ba sosai kamar yadda take fada mana ba. Dole ce ta saka Hana yarda tana soya mana awara a waje ba dan tana so ba, domin ko a lokacin da Mama take gidan kuma muke cikin tsananin shan wahala bata taba gwada dora mana talla ba, amman ita wannan da ba uwarmu ba ta fara dora ma Hana talla daga zuwanta. Ko da yake ba laifinta babne laifin Baba domin shi ya bata dama Hana kuma bata isa tace ba zata yi ba, duk kuwa da kasancewar bata so ko kadan. Domin fita tallar ya kashe mata tafiya makarantar yamma, ya zama boko kawai take iya tafiya da safe. Ni kuma aka bar ni da wahalar aikin gidan, shara wanke wanke da hura wuta tun ban iya ba har na iya, girkin ne kawai bata bari na yi domin na gwada girkanwa ta ji be yi mata yadda take ba. Idan zata hada kunun wanken soyan ni nake wanke goruna ni nake mata komai har tacewa, awara kuma ni zan gyara wake da dare da safe taje ta kanta ta kai nika, idan ta dafa a tare zamu natse ni zan yanka idan aka soya be wuce a ba ni da hansin ba ko saba'in. Wani sabon shafin wahalar rayuwa Umma ta bude mana a idan, ni da Hana saboda sana'ar da take wai ai ba ita zata fita ta yi ba a dole hana zata soya mana wara a waje ni kuma na yi aikin cikin gida. Ta inda nake samun sauki shi ne takaba da nake bana fita, saboda haka duk wani aiki na fita ita zata fita ta yi, da safe kuma Yaya sai ya cika gidan da ruwa sannan yake fita. Ta inda gurin da ta samu banbancin da Mama a zamanta gidan ita kam Baba yana bata abinci da cefane mai kyau, ba kamar Mama ba da wani lokacin zai ce be da shi ko kuma ya bada abinci ya hana cefane ko ma ya hana gaba daya. Wata kila saboda ita din tana da dan da sauran kurciya ba kamar Mama ba, wata kila kuma dokin amarci ne yake Allah masani. Idan kuma aka yi girki ba a ba mu wani abun arziki Allah ma ya sa yanzu damuwa bata barina na ci na koshi kamar da, wani lokacin har ragewa nake na bawa Hana a da kam na fi kowa cin abinci a gidan, ranar da Hana ta tafi family house din Mama ta fada musu halin da ake ciki na dora mata talla, washe gari Kawu Garba ya samu Baba yana nuna masa hakan be dace ba, sai Baba yace kar wanda ya sake saka masa baki akan lamarin yaransa shi ya ga damar su yi, kuma babu mai ciyar masa da yara sai su. A nan yake fadar ai tun kamin auren ya fada mata yaransa za su rika mata wani abun saboda ta fada masa ita fa tana sana'a kuma aure ba zai hana ta yi ba, shi kuma ba zai iya ganin matarsa da aure ta fita waje ta yi sana'ar wara ba, domin haka yarsa zata maye masa gurbi. Ni kam gaba daya na zama kamar ba ni ba duk abun da ake bana iya cewa komai sai ido, wani kalar canji ne ya same ni irin wanda ban yi zato ba. KAREEM POV. Da kansa ya shiryawa yaransa abun karyawa ya dauko lunch box dinsu ya raka su har gurin School bus suka shiga sannan ya juyo ya dawo, dakinsa ya shiga yayi wanka ya shirya ya fito ya shiga motarsa. Family house dinsu ya wuce domin fara gaisawa da iyayensa kamin ya wuce aiki kasancewar yau Monday. Wani abun da ya sabawa kansa da shi ne, na kin kallon mahaifiyarsa a duk lokacin da ya shiga gidan. Kai tsaye ya wuce bangaren Hajiya Hassana wadda take step mom dinsa. Karyawa ya same ta tana yi tare da Khadija da Aaryam da sauran yaransa Aneesa da Kamla. Kanensa duk suka gaishe shi ya amsa, Yusura dake zaune gefe daya ta mike tsaye ta shige dakin Hajiya Hassana sai a lokacin ma Kareem ya lura da ita. Khadija ta kwashi kayan abincin ta bi bayan Yusura Kamla da Anessa ma haka, sai ya rage daga Step Mom dinsa sai kanensa Aaryam. “Zaka ci abincin a zuba maka?” Hajiya ta tambaya. “Aa” “Baka cin abinci yanzu, tun da Momynka bata nan, shigowa nan ma sai monday Monday kake yi ka duba mu, idan Momynka bata nan ni da mahaifinka ai muna nan kuma Kanenka suna nan be kamata kana haka ba” A hankali ya sauke ajiyar zuciya. “Hajiya Bana jindadin shigowa ne yana yawan tuna min da Momy kuma ina jin babu dadi” “Tohm ya za'ayi haka tsarin Allah yake, kai kanka mutuwa zaka yi balle kuma wasu, sai hakuri rayuwa ta gaji haka, ni kaina yanzu gidan ba dadi yake min ba Wallahi, amman a haka nake daurewa saboda Khadija da Aaryam da kuma Aneesah, dole na yi walwala idan ba haka ba dukanmu sai mu taru mu takura mu yi ta bakinciki da kuka” Yayi shiru be ce komai ba. Hajiya ta dauki tissue ta goge hannunta. “Likita..” Ta kira shi sai ya kalleta daman haka take kiransa tun Momy na gidan. “Ni fa ba zan boye maka ba, ban gane manufar abun da ka yi ba, kuma ban gane inda kuka dosa ba” “Na miye ba Hajiya?” “Kai da Yusura mana, ta dawo gida kawai tace mana ka sake ta, saki daya biyu ko uku ba mu sani ba, Daddy ka ma fushi yake da kai shiyasa be maka maganar ba har yau, Khadija da Aaryam ma gashi a zaune kullum haushinka suke ji saboda haka” Kareem ya juya ya kalli Aaryam kyakkyawan saurayi mai jini a jika, sai yayi murmushi. “Saboda Yusura?” “Eh mana, Daddynka cewa yayi ba zai maka magana ba, kuma kar wanda yayi maka a saka maka ido kawai, ita kuma ta so barin gidan ni na hana, saboda na san idan Momynku tana raye Yusura bata da gurin zama sai gidan nan, a nan ta girma nan ta saba yanzu kuma dan Momy bata nan babu wanda zan bari ya dauketa ko kuma ita ta tafi ta bar mu, sai idan na mutu, kai ma dan kana ganin Momy bata nan ya saka kake son ka wulakanta amanar da ta baka, to ka sani Yusura ta fika gata a gidan nan, kuma matukar ina raye ni ce gatanta ba kuma zata wulakanta ba” Kareem yayi gutun murmushi ya girgiza kai, kana ya sake juyawa ya kalli Saurayin Kanensa ya ce. “Fushi kuke ta yi da ni akan abun da Baku san komai a kai ba” Aaryam ya ce. “Haba Big Bro ko dai minene ai be kamata ace ta kai ga haka ba, kai fa Namiji ne, kuma ga yara tsakaninku, kawai dai ban maka magana ba ne saboda Daddy yace kowa ya saka maka ido, kuma ina kasa da kai be kamata na tsuma baki a irin wannan ba sai idan ka bukata” “Gaskiya ne” Kareem ya fada tare da aje numfashi sannan ya mike tsaye ya nufi bangaren mahaifinsu, sai a yanzu ya fahimci dalilin da ya saka har yau da suke wata biyu da sati biyu da rabuwa Daddy be taba kiransa ya tambaye shi miye ya faru ba, kuma be taba yi masa maganar ba a duk shigowar da yake gaishe shi a gidan. A natse ya shiga bangaren kamar yadda ya saba sai bayan da ya zauna sannan ya gaishe da Daddy dake sanye da gilashi yana duba newspaper. “Lafiya Kalau, Kareem ya gidan ya yaran?” “Lafiya kalau Daddy” “Maa Shaa Allah, yau Monday ko akwai aiki” “Haka ne Daddy” “Allah ya taimaka ya bada nasara” “Ameen” Kareem ya mike tsaye har ya fara tafiya sai kuma ya dawo ya zauna yana kallon Daddy. Daddyn ma ya kalleshi “Allah yasa lafiya, akwai wata matsala ne?” Kareem ya hade wani abun da ya tsaya masa a makoshi sannan ya ce. “Daddy, ban ji kace komai akan dawowa Yusura gidan nan ba” Daddy ya aje newspaper dake hannunsa. “Oh wai Yusura, Mijinta ne ya sake ta kasan kuma bata da wani gidan da ya wuce nan, bata da gata a duniyar nan sai mu, zamanta a nan ya takura maka ne? So kake a koreta?” Kareem yayi murmushi jin yadda Daddy yake fadar mijinta ne ya saketa kamar be san Kareem din ne mijinta ba. “Aa Daddy ai ban isa na ce a koreta ba” “Good kara dai da kasan haka” Ya sake yin murmushi, a yanzu ne ya kara tabbatar Daddy fushi yake da shi. “Kawai dai na yi zaton ko zaka bincike abun da ya faru ne” “Abun da ya faru, tsohuwar budurwarka tana zuwan nemanka, amaryar abokinka tana zuwan nemanka ta yi magana sai ka mareta ka ce ka saketa” Dif Kareem ya dauke wuta kamin ya kalli Daddy ya ce. “Haka ta fada maka?” “Ba gaskiya ba ne Daddy, Safeena ta zo gaisuwar Momy ne, kuma na gargade kar ta sake zuwa domin babu wata alaka tsakanina da ita, Noor kuma tana zuwa ne saboda tsabanin da suke samu da Hafiz a lokacin” “Zan yarda da wannan, domin ban san ka da wani aiki na assha ba, shi ma wannan saboda Hassana ta matsa ne ya saka ta fadi wannan dalilin, amman bayan haka bata fada mana komai ba, ni kuma na auna abun a ma'aunin kishi ne, sai dai kai kuma ka yi kuskure na aikata saki a take” Kareem yayi shiru kamar ba zai ce komai ba. Daddy ya cigaba. “Shiyasa na yi shiru na zuba maka ido na gani shin kana da hankali kansan ya kamata ko baka sani baKareem ya sauke numfashi mai nauyi. “Daddy, akwai abubuwan da ni da ita muka boye ba mu bar kowa ya sani ba, ban san ya zaka fahimta ba gaskiya ce mai matukar nauyi da daure kai, Daddy ni da Yusura ba mu taba son junanmu ba, ban taba jin ina sonta ba ita ma bata taba jin tana so na, wannan sakin ma ta dade tana bukatar na yi mata shi, saboda da nisanta da ni” Daddy yayi murmushi mai sauki ya cire gilashin idonsa. “Kareem karka maida karamin yaro mana, baka sonta bata sonka aka yi muku aure kuka zauna lafiya har kuka haihu ba a taba jin kanku ba sai yanzu da Mahaifiyarka bata raye zaka ce wai baka sonta? Wannan ba hujja ba ce” Cikin tsananin damuwa Kareem ya ce. “Wallahi Daddy bana son Yusura ita ma bata so na, kawai dai mun amsawa Momy ne kuma mun zauna saboda ita, ni da ita ba za mu iya bijirewa umarninta ba” “Okay yanzu da bata raye mu ne abokan wasarka? Kai da ita? Ni ba zan ma yarda ba ku son junanku ba. Kareem zan baka shawara karka yarda ka rasa Yusura, na yi aure tun kurciya har yanzu na zauna da mata biyu a lokacin da mahaifiyarka take raye, mu kan samu tsabani mu yi dadi, wani lokacin har iyaye su sani, amman ban taba ganin matar aure da bata taba kuka da mijinta ba sai Yusura, bata fadin sherinka, bata kawo kararka, kai a gurinka ba abun kunya ba ne aji ka saki matarka? Kuna da yara biyu me kake fada musu? Idan aure kake son karawa you're free to do so ba sai ka saki matarka ko ka wulakanta ta ba, idan har kana fadar saboda Mahaifiyarka ka aureta to miye amfanin sakin a lokacin da mahaifiyarka bata raye? Ke nan ganin idonta kake yi ma biyayya ba saboda Allah ba? Yanzu da ban yi magana ba haka zaka zuba ido ta cika idda? Ko saki uku ka yi mata? Domin bata fada mana ko saki nawa ka yi mata ba, kuma ita bata zauna kamar kai ta kalli kwayar idonmu ta fada mana bata son dan mu ba, Kareem idan ka sake ka rasa Yusura ka rasa matar kirki kenan har abada” Kareem yayi shiru be ce komai ba, domin ya fahimci Daddy ba zai yarda da duk wani zancensa ba. “Saki nawa ka yi mata?” “Daya” Sai a lokacin Daddy ya sassauta muryarsa ya daina yi ma Kareem fada. “Ka yi hakuri, shi zaman aure dan hakuri ne, duk can talkaminmu suka tsinke, dole sai an kai zuciya nesa, bana son na sake jin wata matsala a tsakaninku, ka maida matarka dakinta ku zauna lafiya dan Allah” Kareem kamar zai fasa kuka ya ce. “Daddy mai daki shi ya san inda yake masa yoyo...” Be rufe baki ba Daddy ya rufe shi da fada yana masa tsawa. “Get out Kareem, tashi ka dauki matarka ka aje ta gida sannan ka wuce aiki, wato Momy kake tsoro kana gudun zuciyarta mu kuma ka raina mu ko? Toh ka bari har bayan raina sannan ka saketa idan ka ga dama ka hada har da yayanka ka koresu gaba daya” Da sauri Kareem ya sauko daga kan kujera yana bawa Daddynsa hakuri, domin idan akwai abun da yake gudu da tsoro a rayuwarsa to fushin iyayensa ne. “Ka yi hakuri Daddy, na maida aurena saboda kai, kuma zan dauke ta mu tafi gida yanzu kamar yadda ka ce ka yafe min dan Allah” Daddy ya dauke kai ya kai hannu ya dauki gilshinsa ya mike tsaye ya shige bedroom dinsa. Kareem ya dafe kansa ya rumtse ido, ya fi karfin minti talatin a haka sannan ya dago ya fito daga bangaren ya dawo bangaren Hajiya Hassana ya zauna a falon ya kasa yin komai har sai da Step mother dinsa ta fito sannan ya gabatar mata da abun da ya maido da shi bangaren nata. “Na maida aurena Hajiya, a fada mata ta fito mu tafi” Hajiya Hassana ta yi murmushin jindadi. “Haba yanzu na ji magana, ko kai ba haka ake so, kuma dan Allah ayi ta hakuri karka ce zaka biyewa mace ita mai rauni ce, kuma duk matsala da za a samu a daina saurin saki, muna raye idan ya kamata mu ji sai ka sanar mana mu tsawatar mata yafi ayi ta saki ga yara” “Tohm Hajiya” Ya amsa irin amsawar nan na wanda ya rasa interes da mafaka da kuma gata a lokaci daya, daman tun farko yayi tsammanin haka shi ya hana shi sakinta a lokacin da Momy bata dade da barin duniya ba, da ace kuma ya sake a lokacin da take raye Allah kadai ya san irin fushin da Momy zata yi da shi. Ya mike tsaye yana jin wani fever na rufe shi ya nufi motarsa ya bude ya shiga ciki ya zauna yana jiranta bakinciki cike fal a zuciyarsa. Ya bata awa daya a haka sannan Aneesah ta fito ta bude motar ta ce masa. “Big Bro wai Hajiya tace ka tafi zata kawo ta da kanta” “Toh ki fadawa Daddy haka idan na wuce” Cikin tsananin damuwa Kareem yake maganar sannan ya ja motarsa ya fice daga gidan. Wunin ranar aiki kawai yayi dan ya zame masa dole ba dan jikinsa da zuciyarsa suna cikin dadi ba. Bayan ya gama yana kokarin hada kayansa ya wuce wata mate room ta shigo ta kawo masa takardar envelope. “Maman Khalid miye wannan” “Wallahi ban sani ba, wata ce ta zo dazun bata same ka tace bari ta ba ni na aje maka dan Allah kar na bawa kowa sai kai hand to hand” Ta fada cikin hausarta da bata gama kwarewa ba, kasancewarta bayarabiya. Ya karba fuska ba yabo ba fallasa yayi mata godiya ya hada kayan saukinsa ya fice daga office din. Sai da ya shiga motarsa sannan ya bude envelope din wani kamshi mai dadi ya bugi hancinsa, flower ce farkon abun da ya fara cirewa daga takardar sannan wani sexy chocolate da kuma farar takardar mai rubutu red. Be yi tsammanin ganin romantic abu irin wannan ba sai a Safeena kuma ya canka daidai a lokacin da ya fara karanta sakon na karin shekararsa a yau. “Happy birthday Love, barka da zagayowar ranar haihuwar mutumen da bana son zama da kowa sai shi, barka da zagayowar ranar haihuwar mai bani farinciki a zuciya da jiki, mai kwantar da min da hankali, mutumen da ke nisantarsa ke haukata ni ta hana ni sukuni, barka da karin shekara My future husband, my partner in crime, the father of my future kids, father to be... I know its your birthday today.. I am sure u will give me treat in a big house like we use to be.. so I shall talk to you in person there, because I don't know to express my feelings in paper, i love you duk yadda kake tsammanin za mu iya rabuwa da junanmu ba zamu iya ba Kareem saboda muna son junanmu, ba zan iya kyaleka a irin wannan yanayin da kake da bukatar wani a kusa da kai ba, i know how painful it's to lost a best friend and Mother. Please take good care of yourself for me...” Ya girgiza after ya gama karantawa, so today is his birthday gaba daya ma ya manta, daman tun kamin su rabu tun tana girlfriend dinsa ita take tunawa da birthday sai kuma Momy, and even after break up bata daina wishing dinsa ba a duk lokacin da ranar zata zo. Wani gurin ya bude a motarsa ya saka takardar ya rufe ya yi ma motarsa key. Kusan wannan ne karo na farko da yake jin kamar baya sha'awar komawa gidan all his thoughts is Yusura ta koma gidan by that time, hakan ne ya rike shi daga komawa da wuri domin samawa yaransa abun da za su ci da rana wani lokacin daga restaurant yake karbowa ya je musu da shi, wani sa'in kuma da kansa yake girkawa tare da su ko kuma kamin su dawo. He park his car near the entrance ya bude motar ya fito ya shiga falon. To his greatest surprised yaransa suke tarbe shi da wani irin farinciki da murna da ba su taba tarbonsa da shi ba. “Dady welcome home, Dady Mamy ta dawo” Ya rage tsawonsa yana kallonsa da murmushin da ya ara ya yaba a fuska saboda yaransa. “Kun jidadi?” “Eh sosai” Babbar ta fada sai ya shafa kanta, ba su taba tambayarsa ina Mamy su tafi ba, yaushe zata dawo me yasa bata gidan, tun da suka dawo daga school ba su same ta ba ba su sake walwala ba, kuma ba su tambaya ina take ba, kai ka ce sun fahimci sakinta aka yi, tun daga lokacin Kareem be sake kai su family house dinsa ba saboda gudun su ganta ko kuma su yi kuka idan zai dawo da su. “I'm happy too” Ya fada yana kallonsu cike da alfahari, and he's not lie farincikin yaransa farincikinsa ne, hakan kuma ba yana nufin ya jidadin dawowar Yusura ba, idan har akwai abun da yake nadama a yanzu be wuce aurenta ba, me yasa be fadawa Momynsa gaskiya from first place ko da ba zata jidadin haka ba? Yanzu a wa gari ya waya, waye a matsala sama da shi? “Kun ci abinci?” “Eh munci Mamy ta dafa mun ci, naka yana dinning Dady” “Okay bari na je na yi wanka na shirya sannan na zo na ci, ku je ku yi shirin islamiya” “Okay Dady” Karamin ya amsa, babbar kuma sai da ta sumbance shi sannan ta nufi sama da gudu tana murna. Tsaye yayi yana kallonsu har suka haye suka shige dakin Yusura sannan ya sauke ajiyar zuciya ya haura stairs din ya shiga dakinsa. Bayan yayi wanka ya kwanta a dakin yayi bachi awa daya ya farka, bandakin ya shiga yayi alwala ya fito ya saka ya sauya tufafin jikinsa daga kanana zuwa shadda sannan nufi madubi ya dauki dan'uwansa turare ta feshe jikinsa sannan ya dauki wayarsa ya wallet dinsa then car keys ya fice daga gidan gaba daya. A hanya ya tsaya yayu sallah la'asar sannan ya karasa restaurant dinsa. Yana shigowa reception din Nabil da ya gama dutysa zai fita ya gaishe shi cike da girmamawa. Kareem ya mika masa hannu suka gaisa. “Ka gama naka eh?” “Eh na gama ranka ya dade, daman duty safe nake yau, ko akwai abun da zan yi?” “No aa, ka ce ka daina karatu?” Ya gosa kansa cikin jin kunya ya amsa domin abun kunya ne wannan zamanin a kalli matashi kamar shi ace baya karatu a . “Eh Wallahi, amman dai zan koma nan gaba idan Allah ya yarda” “Me ka taba karanta? Wane course?” “Mass Com na fara, amman dai ina son nan gaba idan zan koma na canja course” Kareem ya cigaba da tafiya yana fadin. “Why baka son aikin jarida ne?” “Ina son, amman dai yanzu na fi sha'awar Public health” “Karatun health yanzu yayi yawa, why not ka yi political science? Karatun yana da kyau, kuma idan ka dace da gurin aiki kamin an ankaro ka dauke nauyin gidanku” “To da har ka kawo wannan shawarar da yardar Allah shi zan yi ranka ya dade” Kareem yayi murmushi yana jindadin yadda Nabill yake girmamashi. “Na jidadin haka, ni kuma zan yi kokarin sama maka scholarship, a private ko kuma gov school, ban sani ba ko a samu a nan gida nigeria ko kuma a waje, fatan dai ba zaka ba ni kunya ba” Nabil ya rasa me zai ce ya rika hannun Kareem yana son masa godiya ya kasa domin be taba kawo wani zai dauki nauyin karatunsa ba, wanin ma kuma Kareem. “Ranka ya dade, na rasa me zan ce ma” “Toh ka aje kalamanka sai idan an samu tukuna, sai ka yi godiya” Cewar Kareem yana dafa kafadarsa sannan ya wuce yana murmushi ya bar Nabil tsaye da mamaki. Be yi taku goma ba ya juyo ya kalli Nabil. “Nabil ya Noor take?” Nabil ya hade yawun bakinsa da sauri ya matsa yana amsawa. “Ta.. Tana lafiya ranka ya dade” “Ba wata damuwa babu wata matsala?” “Eh to tana dai cikin damuwa, mutuwarta nan ta dan taba ta gaskiya, domin ta canja gaba daya kamar ba ita ba” Kareem be ce komai ba, ya juya ya cigaba da tafiyarsa. Office dinsa ya shiga sai da ya zauna sai kuma ya tashi yake yi yanzu a duk lokacin da ya shigo, da zarar ya kalli kujerar da Hafiz yake zama idan ya shigo office din da yamma sai ya ji babu dadi. Har yanzu ya gagara sabawa da rashin abokinsa wannan kawa zucin yana nan tare da shi, shi ke hana shi walwala a duk lokacin da ya shigo office din. Be wuce minti ashirin a ciki ba, ya mike tsaye ya dauki keys dinsa ya fice da kansa ya shiga ya saka aka zuba masa abincin da yake sha'awar ci yaron gurin ya rika masa har gurin motarsa. Front seat ya bude aka zuba abinci sannan ya rufe ya shiga bangaren tuki yaja motar ya fice daga restaurant din gaba daya. Tuki yake not knowing what to do or to go, shi dai gashi nan duniyar gaba daya ta ki ta yi masa dadi. Be faka ba sai da ya samu wasu itatuwa dake gefen hanya, ta cikin itatuwan ya ratsa ya faka motarsa sannan ya bude ya dauki abinci yana ci, gurin is so fresh ga wani iska mai dadi babu damuwa ko hayaniyar kowa it's just him and himself. NOOR POV A kwana a tashi babu wuya ga Allah, kamar jiya na fara wanka duk dai wasu sukance wankan be wajaba a kaina ba, saboda ya sake ni, sai dai zancen da ya fi karfi shi ne na yin zaman takaba domin akwai gyara a auren kuma ban kai ga cika idda ba ne ya rasu. A ranar da na yi wata hudu da kwana goma Mama ta aiko da waina da fanke aka raba sadaka yan'uwanta suka zo tare da yan'uwan Baba aka saka ni na yi wanka na saka sabuwar atamfar, a ranar kuma mutuwar Hafiz ta dawo min sabuwa kai kace mun yi shekara aru aru da shi ba yan watanni ba, sai dai abun da ya daure min kai shi ne na rashin zuwan dangi ko yan'uwansa a gurin tun a ranar da na dawo gida har zuwa yau babu wanda ya leko ni ko ya bincika lafiyata, abincin da ake cewa dangin miji ma suna kawowa matarsa idan tana takama basu kawo min ba. Wata kila Aisha ta shafa min bakin fenti a idonsu domin na lura har bayan mutuwar Hafiz kishi take da ni. Bayan sallah Isha'i, a lokacin da kowa ya watse, ina zaune ina gyara wake soya Yaya ya shigo cikin gidan da kuzarinsa ya ce. “Noor oga Kareem ne a waje yace na kira ki” Na yi shiru na wasu dakiku sannan na mike tsaye kamin na cira kafa na ji Umma ta tabe baki tana fadin. “Wannan ai ba mutunci ba ne, ace ana maka sallama ka mike kai tsaye ka fice ba tare da tunanin fadawa mahaifi ba, kai ma ai ba ita ya kamata ka samu kai tsaye ka fada mata ba mahaifinku ya kamata ka fadawa” “Ba kisan waye oga Kareem ba Umma, oganmu ne na gurin aiki kuma abokin mijinta nw Hafiz ya saba zuwa nan akai akai” Ya Nabil ya bata amsa. “Tohm Allah ya kyauta, tashi ki tafi, amman gaskiya idan haka mahaifiyarku ta koya muku ba abun kirki ba ne, ai sai uba ya aminta ake fita domin shi yake aurar da yarinya” A kam ban iya rike kaina ba sai da na mayar mata da martani. “Baki san komai akan uwarmu ba, karki sake fadin wata mummunar kalma akanta” Kallona ta yi ta dauke kai bata ce komai ba, ta cigaba da dakan yajin da take. Ni kuma na shiga ciki na dauko hijab dina na saka na fito kofar gidanmu. Sai na same shi a gurin da suka saba tsayuwa shi da Hafiz idan sun zo, ko kuma idan ya zo shi kadai. Ganinsa ya tuna min da Hafiz sosai sai zuciyata ta yi min babu dadi, shi kuma na lura baya cikin walwala da farinciki, gashi ya rame kamar ni yayi hudu haskensa ya rage. Gambun motar dake bude ya rufe sannan ya jingina da motar yana kallona kamar wanda be taba gani na ba. “Noor how are you now?” Tambayar yake ya nake, amman sai na ji kamar yace na fada masa damuwata ta hanyar kukana. Kawai sai na fara hawaye ina kallonsa, i miss him i miss his friend i miss my previous life. “Kina cikin damuwa ko?” Na daga mishi kai, sai na ji ya sauke ajiyar zuciya. “Duk yadda kike tsammanin abun ya wuce nan Noor, na fi ki shiga damuwa yanzu, i loss hope, kawai ina rayuwa da kokarin tsayawa saboda Yayana, a yanzu babu wani daki da zan iya rufe kaina na ji sanyi, duka dakunan zafi ne da su kamar wuta” Na share hawayena. “Da zan iya komawa na gyara rayuwata ta a baya...” Na ji ya fada sai kuma yayi shiru be cigaba ba. Ni kuma na kalleshi na ce. “Da ka goge shafina a rayuwarka” Ya girgiza min kai. “Ba zan iya goge ki a rayuwata ba Noor ko da kuwa ace ina da wannan damar, ba ki min komai ba, babu dalilin da zai saka na natsane ki, you're just innocent, precious soul, and Hafiz was right akan abubuwa da yawa akanki” “toh me zaka gyara?” Yayi murmushi ya gyara tsayuwarsa. “Ba wannan ya kawo ni, na zo nan ne saboda na yi magana da ke da kuma Baba, amman kamin nan fada min ya kike?” “Ina lafiya, amman mutuwa bata da dadi Kareem, shiyasa lokacin da Hafiz ya fada min mahaifiyarka ta rasu, na yi kuka sosai na tausaya maka yanzu kuma na ji yadda ake ji” Murmushi yayi ya daga kansa sama sai kuma ya sake kallona. “Noor... Kamin na manta, na zo nan ne saboda maganar gadonki da kuma kayan dakinki” Na cigaba da kallonsa ina sauraren abun da yake fada. “Noor dan Allah karki ce zaki yi jayayya da iyayen Hafiz akan gado ko wani abu, sun ce baki da gado kanensa ya kira ya fada min kuma na je na same su na yi musu magana na fahimtar da su, amman ba su yarda ba, iyakar hujjarsu wai Hafiz ya sake ki kamin ya rasu, kuma kamin ya sake ki wai be taba tarayya dake ba haka ne?” A nan na sauke kaina kasa na dan bata rai. “Aisha ta bata ni a gurin kowa, kuma ita ce silar duk faruwar haka” “Babu wanda zai iya bata ki a gurina, kuma mutuwar aure abu ne da Allah ya kaddara, kuma ba dan Allah ya rubuta haka ba, na yi magana da Hafiz kuma yayi alkawarin yana dawowa zai zo ya dauke ki ku tafi gidan tare, sai dai kamin ya iso Allah yayi ikonsa” “Da gaske?” Ya daga min kai. “Yes Noor na lura kina cikin damuwa a lokacin kuma kin fada min kina son komawa ai, babu wani abun da zaki roka ban miki shi ba Noor sai idan ba zan iya ba” “Na dauka ina takura maka ne, na ga har baka son zuwana gurinka, na san ni ina da takura ai” Yayi murmushi. “To ki yi hakuri, idan Baba yana ciki shiga ki masa magana” “Baya nan yana majalisa” “Shiga ciki zan je can na same shi, ki kwantar da hankalinki Allah zai baki abun da ba su ba ki ba, kayan dakin ma sun ce ba za su baki ba ai saboda shi yayi komai” “Ni fa ba abun da ya dame ni da wani gado, su je su yi ta riko, amman ka yi magana da Baba shi ne dai na ji yana zancen zai yi kara idan ba a bada ba” “Okay” Kallona yake har na shige cikin gidan, ina shigowa Ya Nabil ya fita waje.”Duk wata maganar da zai yi da Baba na san ba zai saurare shi, amman kudi za su iya sakawa ya fahimci komai kuma ya sassauto. Da alaka kuma Kareem yayi amfani da su ne domin babu ya shigo da far'a har da tsarabar nama yayi ma Umma. Cewa yake a yanzu ya hakura zai kyalesu amman saboda Kareem be kawai ba dan haka ba da babu abun da zai hana shi jan min hakkina. Yanka biyu aka ba mu, sai da muka cinye sannan yayi mana albishir wai Kareem ya fada masa ya nemawa Ya Nabil karanta a Sudan. Farinciki ya cika ni a lokacin da Baba yake fada min Kareem yana neman izininsa idan ya aminta sai ya fadawa Ya Nabil din ya kai masa takardunsa na SSCE. Sanin da na yi ba karamin dadi Ya Nabil zai ji ba, ya saka ni farincikin da na kwana biyu ban yi ba. Hakan kuma ya karantar da ni cewar Kareem yana da kirki ta wani bangaren, domin gashi ya danne kudirin mahaifina kuma yana kokarin nemawa dan'uwana karatu alhalin be hada komai da mu ba. Farinciki a gurin Yaya Nabil ba a magana kamar zai zuba ruwa kasa ya sha domin murna, daman abun da yake nema ne yana son karatu shi da Hana ba kamar ni ba. Washe gari da safe Kanen Hafiz ya sake kawo min ziyara sai dai wannan karon ba, maganar gado ce ta kawo shi ba, ya zo min ne da tsaraba ta atamfa biyu da kuma turare sai sabulu da talkami da kudi 10k wai yana taya ni murna fita waka, kuma na yi hakuri da yadda yan'uwansa suka nuna min halin ko'ina kula. Na karba na yi masa godiya muka yi sallama na shiga ciki, bana tunanin ina da wata bukata ta kudi a yanzu wannan ya saka na dauki kudin na bawa Hana na ce ta kaiwa Mama idan ta tafi gidan, domin ita ce mai yawan zuwa ni ban taba zuwa ba domin an yi auren ne a lokacin da ba ni da halin yawo. Abu kamar wasa, shiryen shiryen tafiyar Yaya Nabil Sudan ya fara, duk wani abu da za'ayi Kareem ne yake ba shi kudi yayi, har aka kammala komai within three months. Ranar da zai je yi ma Mama bankwana na bi shi muka tafi tare, ni da shi sai a ranar muka fara zuwa gidan. Babba gida ne mai bangare kusan hudu, gida ne mai kyau da tsari Mama da kanta na san ba ta taba mafarkin aure irin wannan gidan ba. Da muka shiga ciki sai ta zame mana kamar wata bakuwarmu saboda yadda rayuwa ta canja mata, ta yi kiba ta kara haske ga tufafi masu tsada kayan kallo kai har da dinning da ac kamar daman can Mama bata taba auren talaka ba, duk inda ta wulga kallonta nake kamar wata bakauya. “Noor na zame miki sabuwa yanzu ko?” Na yi dariya ina kallon plate din taliyar da ta aje min nama batsa batsa kamar wanke. “Mama ina ta mamaki ne, ina kika hadu da wannan mutumen ne?” Ta dan hade rai. “Mutume? Toh idan ba zaki iya kiransa da Baba ba, ki kirashi da suna Alhaji kamar yadda kowa yake kiransa a gidan nan, wato ke dai sakarcin ki ba zai canja ba ko?” Na yi shiru ina kallon Yaya dake cin taliyar, sannan na soma cin tawa. Rabin abincin kawai Yaya ya ci ya sha ruwa yace zai tafi. “Da wuri Nabil na yi zaton sai dare, saboda Alhaji ya dawo ku gaisa, yana ta fadar ban taba gabatar masa da sauran yarana ba, be san kowa a cikinku ba sai Hana da ke yawana zuwa” “Bana son na kai dare Mama, akwai guraren da ya kamata na tafi kamin ba bar garin nan, kuma kin ga kwana biyu ya rage min” “To sai dai kai ka tafi Noor kuma zata tsaya sai ya dawo kun gaisa tukuna ta wuce” Mama ta shiga dakinta ta dauko masa babbar leda cike da kaya sannan ta danka masa 20k tana ta sakawa Kareem albarka wai daman a yanzu tana ta tunanin wace makaranta zata nemawa tarin kudin da take shi take yi ma, amman gashi ya dauke mata nauyi. Bayan Ya Nabil ya wuce muka zauna da Mama muna hira take tambaya ko Zafeer ya ji rayuwar Mijina. “Zai iya ji tun da iyayensa suna cikin unguwar, ko basa nan ma ai yan gulma suna nan, fitowar nan ma cewa suke ta yi hakkinsa ne” “Zafeer yana sonki sosai, zai iya dawowa yanzu ma, wata kila kuma iyayensa su hana shi, ko da yake a can baya ma sun yi ta kokarin hana amman ya nace sai ke, gashi kuma an watsa masa a ido, Wallahi mahaifinku be kyauta ba” “Baba ma da yace be yafe ba idan na sake masa magana, shi ne abun da ya fi damuna” “Wai har yanzu? Toh ai Hafiz din baya raye kuma, yanzu idan Zafeer ya dawo ba zai bari ya aureki ba?” “Ban sani ba, amman da kamar wahala saboda yana ganin Zafeer talaka ne” “Haka ne, ubanki be ji wani yare sai na kudi, gashi babu mai iya ja masa liyi a dangi komai yayi daidai ne a idonsu” Na daga kai ina kallon POP din falon. “Taso mu tafi ki gaisa da mutanen gidan, suna ta tambayar, da kika fita wanka ma sai da matarsa tace zata tafi ta duba ki kuma Allah be yi ba” “Ita bata kishi ne Mama?” “Ana tabawa mana ayi mace babu kishi, amman boyewa ake na ciki na ciki, ita dai tana da kirki ba kamar wasu ba” “Ko dai irin na Aisha take miki ba, haka take nuna min ba komai ashe wayo take min” “Ke dai da halinki Noor, na san ki ba, kuma zamanmu a nan Alhaji ya fada mace kamar riga take a wuyansa duk wanda ta daga masa hankali cire ta kawai zai yi ya aje, duk tarin yaransa babu wanda uwarsu take cikin gidan nan, sai wannan matar da yaranta uku, sauran duk iyayensu sun fita, ni ma sai bayan auren nake ji, wata kila shiyasa ta kama kanta” Ina jin haka na san an gudu ba a tsira ba ne, kenan ita ma idan ta yi masa ba daidai ba zai iya sakinta. Daga bangaren Mama muka fito muka shiga bangaren matar da take gidan a yanzu. A cike muka samu falon da mata da maza, Mama ta yi sallama suka amsa suna gaisheta da mutunci. “Noor Ya hakuri?” Wata budurwar da ban waye ta ba ta fada sai na amsa da Alhamdullahi na gaishe da Hajiyar. “Lafiya Kalau Noor, an fita wanka ko? Tohm Allah ya bada hakuri ya kawo na gari” Mama ta amsa da Ameen. “Alhaji ne be santa ba sai mita yake ina boye masa yara, tare da yayanta take jibi zai wuce Sudan gurin karatu, ya zo bankwana amman be tsaya ba, ita kuma ba ce ya tsaya ta gaisa da yan gida” “Ta kyauta gaskiya, da ma dai kin maido nan kila zata fi jin sanyi kin san gidan na mu cike yake da mutane” “Mahaifinta ne ai be yarda ba, ko takaba a nan ya so ta yi amman uban yace ba zata yi ba” “Kin san wasu mazan akwai kishi” Haka dai suke ta hirarsu ni dai kaina na kasa ban dago har sai da na ji an bude kofar falo alamar mutum ya shigo. Dagowar da na yi sai muka yi ido hudu da Safeena tana dauke da cikinta da be gama girma ba. Bata kallon kowa sai ni ni ma kuma bana kallon kowa sai ita muka rika kallon kallo wata kila ita ma tana mamakin ganina ne kamar yadda nake mamakin ganinta. Gidansu ne? Ko kuma zuwa ta yi? Ko kuma dai tana da wata alaka ce da mutanen gidan? “Kin dawo Safeena?” Hajiyar ta fada sai Safeena ta amsa mata ba tare da ta kalleni ba, har lokacin ni take kallo. “Na dawo Hajiya, na karbo files din gobe zan tafi asibitin na kai” “Toh Allah ya taimaka ya raba lafiya” “Ameen” Ta amsa sannan ta dauke idonta ta zauna a kujerar dake facing dina, sai kuma ta sake dasawa daga inda ta tsaya. “Anty Safeena kin santa ne?” Na kalli mai tambayar wata kila su ma sun lura da kallon da take min yayi yawa. Ga mamakina sai ta amsa da cewar “Aa ban san ta ba, wacece hala? Ta yi min kama da wata kawata ce ta yarinya” “Noor ce yar wajen Anty Amarya, wanda mijinta ya rasu” “Allah sarki Allah ya masa rahama” Ya juya tana kallon Mama dake amsawa da Ameen sannan ta sake kallona. Har muka baro bangaren babu abun da take sai kallona kamar wata bakuwarta. Ban kuma san dalilinta na boye cewar ta san ni ba. A bangaren Mama na koma na zauna har dare ina jiran dawowar mijinta saboda mu gaisa, be shigo ba sai bayan Magariba a lokacin da ake hada hadar Sallah Isha'i. Na yi mamakin yadda yayi murna da farinciki ganina babu wata kyama, har na na yi sha'awar ina ma ace shi ne mahaifina ba Baba ba, zaunawa yayi a falon yana ta min nasiha akan hakuri da rayuwa na halin da na samu kaina da kananan shekaru, na yi masa godiya ya saka hannunsa aljihu ya ciro 10k ya ba ni. “Aa na gode” A bakin gaskiya ta ba zan karba ba, domin ko na karba ban san miye zan yi da su ba a yanzu. Sai dai na lura hakan be masa dadi ba domin rufe ni yayi da fada a dole na karba na yi masa godiya. “Tafi bangaren Hajiya ki ce na ce cikin yaran nan duk wanda yake nan ya sauke ki gida” “Tohm” Na mike tsaye na yi ma Mama sallama sannan na fice daga falon yana ta kallona. Bangaren Hajiyar na dawo na sanar mata abun da Alhaji ya fada sai mutumen dake tsaye a gabanta yayinda take zaune ya juyo ya kalleni. A nan ma wani mamakin ya kara kama ni, mutumen nan da ya taba yunkurin biya min kudin siyayyar da na yi a wani dare da muka fita tare da Hafiz. “Kamar na sanki?” Na bude baki kamar zan yi magana sai kuma na yi shiru, ban san me zan ce ba, ni dai ina da saurin gane mutane shiyasa na gane shi. “Noor ce Yar wajen Anty Amarya ce, ita ce wadda mijinta ya rasu” “Ai ban sani ba, Allah ya jikanshi da Rahama” “Ameen, ku tafi tare sai ka sauke ta ka wuce, Noor bari ga Abdull zai fita yanzu sai sai ya wuce da ke, ki jira shi a waje” “Okay” Na juya na fito daga ciki, ban san wacece motarsa a cikin motocin gidan ba dan haka zauna a balcony har ya fito. “Kika zauna a kasa?” Bance komai na na mike tsaye na bi bayansa muka isa gurin wata sabuwar mota, sai da ya fara shiga sannan na bude na shiga front seat. Ba tare da yace min komai ba yayi reverse ya fice daga gidan. “Ina ne unguwarku?” A lokacin da na dago sai na ga idonsa akaina suke. Na fada masa na sake maida kaina kasa kamar ba ni ba. Na ji lokacin da wayarsa ta yi kara ya amsa. “Hello Safeena...” Sai kuma yayi shiru, yana sauraren abun da ake fada masa. “Yanzu na fito gida, amman zan biya ta can, sai na zo miki da shi, shi kadai kike so ko da wani abun?” Na yi shiru ina saurarensa kamar wata Munafuka kamin na ji ya ce. “Okay sai na dawo” Ya aje wayar ya dago zan kalleshi idona suka fada cikin nasa da sauri na dauke kaina ina jin sautin murmushinsa. Ban sake kallon gefen da yake ba har muka isa unguwar. “Ka sauke ni a nan unguwar bata da kyau can ciki” Na fada. “Karki damu, amanarki aka ba ni sai na kai ki har gida” Yadda ya fada haka ya aiwatar har kofar gidanmu ya isa da motarsa ya faka, ni kuma na bude na fito zan rufe kofar ya ce. “Ba godiya” Ban ce masa komai ba na rufe motar, na gode masa sai ka ce rokonsa na yi ya kawo ni. Sai da na shiga gida sannan na ji motarsa ta bar kofar gidan. KAREEM POV. Yana gama sallah asuba ya shiga kitchen hadawa yaransa breakfast. Domin Yusura bata musu komai tun da ta dawo gidan, Kullum shi zai hada musu breakfast ko kuma ya saka aika musu daga restaurant dinsa kamin su tashi break. And now cooking is one of his favorite things, yana samun nishadi a girkin, musamman idan yaran suka farka suka same shi a kitchen suna hayani yana aikinsa har ya gama, ya karya tare da su wani sa'in kuma ya zuba musu na su, ya tafi da nasa a office ko kuma su su tafi da na su school shi kuma ya ci a gida. Idan ya fita sannan Yusura take saukowa ta gyara ko'ina ta dora na rana. Tun da ta dawo gidan be taba leka dakinta ba, be taba ce mata uffan ba, ita ma kuma bata bari sun hadu ba, da zarar ta ji motarsa ko ta san lokacin dawowarsa sai ta shige dakinta. Yau ma sai da ya raka su har gurin bus sannan ya dawo ya zauna ya ci nasa breakfast. Bayan ya gama ya mike tsaye ya shiga dakinsa yayi wanka ya shirya cikin kananan kaya ya fito yana rike da lab coat dinsa da wayarsa sai kamshi yake zuba. Yayi kyau sosai ramar da yayi ta kara masa kwarjini da haifa. Sai da ya fice daga falon sannan Yusura ta sauko a zatonta ya fice gaba daya, dinning ta nufa ta tsaya tana kallon kayan karyawar da ya shirya, biredin da ya gasa ta dauka taba tabe baki ta shinshina ta aje. Sannan ta ja kujera ta zauna ta bude flask din ruwa zafi, a daidai lokacin Kareem ya turo kofar falon ya shigo domin daukar wallet dinsa da ya manta a dakinsa. Kallo daya yayi ma gurin da take zaune ya dauke kai ya haura sama ya dauko wallet dinsa ya sake fice. Yusura bata taba jin kunya irin ranar ba, bayan amincewa da aurensa da ta yi wannan ne abu da na biyu da take bakinciki a rayuwarta, ji ta yi kamar ta fasa komai na gidan dan bakinciki. Tuki yake a hankali har ya isa asibitin, ya faka motarsa a gurin da aka rubuta Dr Kareem sannan ya fito ya dauki kayansa ya rufe motar ya shiga cikin Babbar asibiti ana miko masa gaisuwa yana amsawa. Office dinsa ya shiga ya fara duba takardun dake gurin sannan ya fita ya fara duba marar lafiyar da aka aje da ya kamata ya duba su. After ya gama ya dawo ya zauna a office dinsa patient din dake shigowa suka fara shigowa yana dubata. Third person da ta shigo ita ce Safeena, tana sanye da dogon Hijabinta har kasa sai dai hakan be boye cikin dake jikinta, har ta zauna ita yake kallo. Sai da ta aje jakar dake hannunta sannan ya jingina baya ya kwanta jikin kujerar yana kallonta. “Wai ke wace irin yarinya ce Safeena?” “Ni din wata yarinya ce, mai wuyar warke ciwo, wata yarinya ce da ka koyawa soyayyarka kuma kake kokarin guduwa bayan ka yaudareta da farko” “Gargadin da na yi miki, da kuma tazarar da na baki daga lokacin da muka yi haduwar karshe zuwa yau bata fahimtar dake, na rumgumi kaddarata, ke ma ki rumgumi taki?” “Ka rumgume kaddara saboda Yusura tana sonka tana kyautata maka a yanzu? Ko kuma daman can karya ka yi min kace bata kula saboda kullum ka rika samun biyan bukatarka da ni? Ka yi breaking heart dina da farko yanzu kuma bayan na saba mu'alama da kai na saba da kwanciya a kirjinka na saba da soyayyar kake tunanin sake guduwa ka bar ni?” Ya mike tsaye daga zaunen da yake ya nufi windows dinsa ya bata baya. “Kana da kyau, Kareem kana da kudi amman duk wannan be tabbatar min da ina sonka ba sai da mu'amala ta hada mu, all this while na kyale ka ne saboda ina dauke da cikin nan” “Me kika zo yi yanzu? Tashi ki fice daga office din nan” “Baka da wannan damar ba saboda da kai na zo ba, saboda cikin nan ne, na dawo da awon cikin nan a nan ne, a nan zan yi ta zuwa har zuwa lokacin da zan haihu” Ya dafa Window ya rike kansa. “Namiji zan haifa suka ce, kuma ina alfahari da haka” Kareem ya dauki lokaci a haka kamin wani tunanin ya zo masa sai ya juyo da sauri ya kalli cikin na ta sannan ya kalli fuskarta, sai ta yi masa murmushi. “Fita ki bar office din nan” Ya nuna mata kofar, zata sake magana da daka mata tsawa har sai da ta zabura. “Fita ki bar office din nan na ce” Ta mike tsaye da sauri ta dauki jakarta tana kallon yadda ya hade fuska kamar be taba ganinta ba, ta fice daga Office din. Dawowar yayi ya zauna kan kujerar ya dafe kansa ya runtse ido yana numfashi da karfi, ya girgiza kai kamin ya daga hannunsa ya buga a tebur din yana jin wani irin bakinciki marar misaltuwa... It could be a joke maybe tana gwada shi ne, if not ai tana da hankali matukar ba wata manufa take da ita akansa ba ba zata taba sha'awar haihuwa da shi alhalin tana da aure ba, ta dauki dawainiyar cikin da ba na mijinta ba ta kai masa yayi komai, ba zata fara ba. Abun da zuciyarsa ta raya masa kenan har ya ji ya samu saussaucin cigaba da aikin da yake. Sai da lokacin tashi aikinsa yayi ya tuna da ba shi da abokin hira ko shawara a yanzu domin Hafiz is no more balle ya fada masa hasashensa ko damuwarsa.https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0 PAID PAGE 2️⃣0️⃣ ©KhadeejaCandy ©®Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Rumgume hannayena na yi ina kallonsa with my innocent face. “Besty how are you?” Ya tambaya yana daga kai ya kalli harabar unguwar. “I'm good and you?” Ya daga gira not happy not sad. “I'm not fine” Na dan matsa kusa da shi. “Me ya same ka?” Sauke kai yayi kasa sannan ya ce. “Bestyna kamar kin taba fada min sunan wanda zaki aura ko?” “Eh Abdull” Ya dago ya kalleni. “Yana da mata kika ce idan ban mata ba” “Eh da yara uku matarsa ya haihu na hudu” Ina jin sautin hade yawunsa. “Amman kin taba ganin matarsa?” Na dan kawar da ido daga kallonsa sannan na amsa. “Eh na taba ganinta ya nuna min hotonta” Ya langwashe halshensa. “Kin san sunanta?” “Safeena your ex-” Murmushi yayi ya jinjina kai yana juya idanuwansa like na bashi mamaki sosai, kamin ya kalleni. “Kin san duk wannan kuma kika yarda zaki auri Abdull?” “Ba mutumen kirki ba ne?” “Ban san komai a kansa ba, amman na san komai akan Safeena, ba zaki iya kishi da yarinyar nan ba, she's criminal” Na dan tabe baki. “Bana jin zata yi kishina, ai kai take so kuma kai take kishi, me zai saka ta yi kishin mutumen da bata so indai har da gaske bata son shi” “Mijinta ne uban yayanta taya ba zata ji kishi ba, kuma ni ban taba fada miki cewar bata son shi ba, taya zata ki mutumen da shi ya tsamota daga ruwa a lokacin da na jefata?” Na daga kafaduna not knowing what to say yanzu kuma. Ajiyar zuciya ya sauke ya kwantar da murya ya ce. “Noor me kika fadawa Safeena?” Na kalleshi da sauri daman na san za a zo gurin. “Me tace na fada mata?” “Sirrin da na yi dake ta zo ta fada min duk abun da kuka yi, saboda me zaki nuna mata cewar kin san abun da yake tsakaninmu” Na ciro wayata daga aljihun rigata na nuna masa sakon da ta turo min, kamin wani abu ya tsikare ni kamar zan yi fada na fara magana. “Ganin na yi tana neman daga min hankali tun kamin na shiga, ni kuma ba na yi aure ne saboda na je na fito ba, bana son aurena ya sake rabuwa sai idan mutuwa ta raba” “Amman sai ki yi amfani da wata hanyar ba wannan ba, ke yarinya ce, baki gama fahimtar duniya ta mutanen cikinta ba, ba ki san illar abun da kika ba sai bayan ki aikata” “Ba ni da wani weapon na yakarta sai wannan” “Amman wannan sirrina ne, na fada miki ne saboda na yarda dake and i need someone to talk to, taya zaki aikata abun da zai iya janyo matsala ya janyo miki?” Zan yi magana ya daga min hannu ya nuna min yatsa. “Look Noor ina da yara, mahaifina yana raye ina da yan'uwa da abokaina, ko kadan bana son abun da zai zubar min da mutunci, na fada miki damuwata ne saboda na yarda dake, kuma ina jin kusanci da zuciyata, ba dan ki bayyana ma duniya ba, na san na aikata abun a lokacin da idanuwa suka rufe shekaru suka tsirewa tunani, and now i realize na yi wa kaina babbar barna and i regret it, you shouldn't discuss this with anyone!!” Ya bude motarsa ya shiga ya bar ni a tsaye ina kallonsa hawaye na sauko min, domin be taba rufe da fada irin na yau ba. Har yayi baya sai kuma yayi gaba ya faka a inda ya faka dazun ya sake bude motar ya fito ya tsaya kusa da ni. “I'm sorry, Na san na kaurara amman Noor ban ji dadin abun da kika yi ba, wannan sirrina ne, be kamata kowa ya ji ba ” “Bana hira da kowa, ban taba fadawa kowa ba, kuma ita wanda ta ji daman ai ita abun ya shafa” Na bashi amsa cikin sautin kuka. Idonsa ya sauke kasa yana sake fuskarsa. “Bana nufin sakaki kuka ko kara miki damuwa akan wanda kike ciki, amman ni abun da kika aikata yanzu zai daga min hankali ya saka ni a damuwa, waya sani ko zaki sake fadawa wani? Kuma Safeena ba zata zura miki ido hakan nan kawai ki cigaba da rayuwa a free ba, bayan kin san sirrinta, ni da ita duk muna da iyali, ki rika duba wannan kamin ki aikatawa wani abun Noor” Na share hawayena. “Ta je ta bata ni gurinka ko?” Ya rufe ido yana murmushi sai dai hakan be hana ni fahimtar damuwar dake shimfide a fuskarsa ba. Bude ido yayi yana min magana a hankali. “Bata iya wannan, babu wanda zai iya wannan ma, just be careful yanzu Safaeena tana kiyayya dake ta kofa uku ne, Allah ya tsareki kuma ya baki zaman lafiya, amman Bestyna Noor ina son ki sani ko mutuwa na yi bana son na tafi na barwa ƴaƴana abun kunya” “Ni ma ba zan so haka ba, kuma na maka alkawari daga wannan ba zan kara ba, kuma babu wanda zai ji” Yayi tattausan murmushi da ya kara masa kyau. “Thank You, Allah ya tabbatar miki da alheri” “Ameen” Ya sake Bude motarsa zai shiga. “Shikenan tafiya zaka yi?” Ya juyo “Ko kina da bukatar wani abun ne?” Na girgiza kai. “I will miss you alot” Yayi murmushi ya sauka kansa. “Akwai abun da kike bukata na auren Noor? Akwai abun da Baba be miki ba?” Na girgiza masa kai alamar aa. A ganina kamar be kamata na dora masa nauyin komai ba, kuma ai da kunya na bukaci kayan daki a gurinsa, domin su ne kawai nake saka ran Baba ba zai yi min ba, shi ma kuma ba ni da tabbaci. “An yi komai” Yayi murmushin dake nuna kamar be aminta da ni ba. “Sai wata rana” Wannan karon be sake kallona ba ya shiga motarsa yayi mata key ina tsaye ina kallonsa har na daina hango shi. Wata kila shi kam ba zai yi marmarina ba kamar yadda anke jin kewarsa tun a yanzu, ba mu wani dade a tare ba amman shakuwa mai karfi ta shiga tsakanina da shi. Bayan tafiyarsa ne fahimci na yi katobara na bayyana ma Safeena na san komai a tsakaninsu ba dan ita ba, sai dan shi wata kila hakan zai iya haifar masa da matsala, sai dai iya abun da na sani shi ne, Safeena ba zata yarda asirinta ya tonu ba, domin tana da aure da yara kamar yadda ya fada, ni kuma ba zan sake tattaunawa da kowa akan matsalar ba. Hakan da na yi ya saka na samu yanci gurin Safeena, mijinta ma ya samu kwanciyar hankali domin ana sauran kwana biyu a daura aure nake tambayarsa ya Safeena sai yake cin yanzu ai ta fahimci, tashin hankalinta ba zai hana aurenmu ba ta shafa masa lafiya. A raina na ce ko dai ta fahimci Ni din ba kanwar lasa ba ce ta bawa kanta lafiya da ni. A daren ne yayi ta damuna da maganganu da be sana yi min ba, hakan kuma ya raunata yarda ta ya haifar min da tsoro akansa, sai dai na lura shi kam sam baya kunyar fadar haka, wata kila saboda ya taba auren ne, ko kuma yayi zaton a aurena na farko na san komai kamar shi. A yadda na lura Abdull irin mutanen nan masu masara kunyar ido da furta komai a take. Ni dai bana iya cewa komai idan ya jefeni da wani kalamin, na kan ji kaina yayi girma kunya ta rufe ni. Washe gari gidanmu ya cika da yan'uwa mahaifina wadanda suka zo shirye shiryen abubuwan da za'ayi, ta hirar da Baba yake da su ne na ji yana fadar mai gidan Nabil wato Kareem yana da kirki da mutumci sosai. “Yanzu bayan daukar nauyin karatun yaron nan da yayi, auren nan da za'ayi sai da ya same ni a majalisa ya damka min kudi mai yawa wai na kara na yi hidima, Allah dai yayi masa albarka ya yara masa yaransa, wutar nan ma da ta taso tsakanina da yan'uwan Hafizu shi ya kashe ta” “Ai wasu masu gida haka suke da taimako da kirki, musamman idan sun san baka da shi, wasu kuma suna bakincikin abun da zaka samu ma” Cewar Baba Garba. “Haka ne, ni farko ma na dauka shi zai ce yana son Noor ne, kuma na ga kamar ba haka ba ne, ai ba dan kar ta ba ni kunya irin na wacan karon ba, Wallahi da sai na aura masa ita saboda kunyar abun da yake min, ya rike amanar abota” Jin hakan a gurin Baba ya saka na ji Kareem ya kara kima a idona, tabbas shi din mutumen kirki mai son taimako, babu ruwansa da duba matsayi ko girma. Haka dai na yi ta jin suna ta hirarsu ta yan'uwa yana fadin mutanen da suka taimaka masa a yanzu da kuma aurena na farko. A lokacin da suka dauko zancen abubuwan da zai kai na ji Baba Garba yana tambayar Baba. “Toh yanzu kai Magaji ka siyo mata kayan dakin ne?” “Ni babu abun da na siya kuma babu abun da zan siya, ai ya fada mana da zarar an daura aure za su wuce can Lagos din da ita, to taya za a tsaya wani siyen kaya nan tun da nan za su zauna ba? Dubu hansin zan bashi a cikin kudin sadakinta idan sun je can ya siya mata abun da ya kamata” Anty Larai ta ce “Aa gaskiya be dace ka yi haka ba, ai ana son ka siyama yarka girma, ko dai ba mai tsada ba kowa ya san karfi ba daya ba, sai ka mata na iya karfinka saboda Allah magaji” “To wai me za'a siya ma? Uwarta ta aiko mata da kaya, kuma ba a nan za su zauna ba, ai kayan sun isheta komai” “Kayan da ta aiko mata kayan kitchen ne, kai kuma naka kayan daki ne da dan wani abu da za aka bawa ango” “Aa aa aa karya haram ba zan iya kashe kaina ba, yarinya suka ce suna so ita za a ba su, ita da Allah yayi jininta jinin masu kudi me zai kai ni wahalar da kai na siye wasu kayan daki? Hafizu ma Allah ya masa rahama da kansa yace ba zai na yi komai ba ya dauke min komai” “Toh shi wannan ai be ce ba, gaskiy...” Bata karasa ba Baba ta tari numfashinta. “Ni fa dan abun da na samu, gyaran gidana zan yi na kuna kallon yadda gidan nan gaba daya ya canja babu wani taimako da na samu, sauran kuma sai na bude shago na zuba kayan masarufi” Jin cewar Baba ba zai yi min furniture ba ya disashe farinciki dake zuciyata, wata kila shi din ba kamar Hafiz ba ne da zai ce ya yafe komai, hakan kuma wani abun gori ne a gurina da danginsa da ma kishiyata. A ranar aka yi min kunshi mai kyau mai ja sosai, da dare kuma Hana da kawata Zainab suka raka ni na tafi gurin gyaran gashi domin ni ba mace ce ma'abociyar son kitso ba. A nan na samu damar fada musu damuwata, Hana ta nuna damuwata da jin cewar Baba ba zai siya min komai ba har ma take cewa. “Yanzu da ace Mama bata aiko da wannan ba haka za'a kai ki ko spoon din aiki ba ki da shi?” Na sake jin babu dadi domin Baba baya kyautata min a rayuwa, wasu hakokan da ya kamata uba ya saukewa yarsa shi baya sauke min su. “Noor kar hakan ya daga miki hankali, Baba ya fadi gaskiya idan ba nan za su zauna ba, babu amfanin siyen kaya, daukar kaya daga Kano zuwa Lagos wani aiki ne babba, kuma kin ga yace ba a nan za su tare ba” Zainab ta shiga kwantar min da hankali, na dube ta na ce. “Amman wasu ko ba a garin za su zauna ba, ana yi komai Zainab a garin da miji yake, saboda can aiki yake yi ai, wata rana zai iya dawowa mahaifarsa” “Ki gode Allah Noor, idan mijinki mai sonki ne duk ba zai ga wannan ba, kuma zai rike ki amana, idan ma Baba bai miki ba ke zaki iya yi ma kanki ko kuma shi mijinki yayi miki, dan Allah ki kwantar da hankalinki Noor” Duk yadda zata karfafa min guiwa sai da ta yi har ta yi nasarar kwantar min da hankali na dan sake raina. A napep muke ta labarin Zafeer da sabon auren da aka ce yayi a gurinta nake jin labarin irin hidimar da aka yi na bikin auren domin Zainab tana abota da kanwar Zafeer sosai, shi ma kuma yana good time da ita ko a lokacin da muka samu matsala ita yake aikowa gurina. “Amman kin ga yana dariya?” Na tambaya ina jin bakinciki marar misaltuwa kamar ba ni na fara guje masa. “To zai ki dariya ne Noor? Ai dole yayi farinciki ko yaya ne, wata kila ma yanzu ya manta da soyayyarki, domin yar masu kudi ya aura ance mahaifinsa ma shi zai sama masa aiki, daman ita yarinyar tana aikinta, ance ta girme shi da shekara uku” “Allah ya saka masa tun ba ayi nisa ba, ya samu wadda ta fi ni komai” Na fada hawaye na sauko min, Zainab ta dube ni. “Noor har yanzu kina son Zafeer wai?” “Unconditionally, har abada zuciyata ba zata daina son Zafeer ba, ba zan taba son kowa kamar yadda na so shi ba” Shiru ne ya biyo baya babu wanda ya sake cewa Uffan daga ni har su. Har muka isa gida hawaye nake, haka na shiga gida rai babu dadi zuciya na kuna, kiran da Abdull yayi ta min ma kasa dagwa na yi saboda damuwar data haifar min da ciwon kai. Washe gari ya Friday gidanmu ya cika da makota da yan'uwa na kusa da nesa maza da mata, kusan wannan bikin ma kamar ya fi wacan yawan jama'a. Bayan saukowa daga Massallaci na fita waje na yi alwala na shigo dakinmu kenan wayata ta yi kara, dubarwa da zan yi sai na yi arba da number Abdull, a take na amsa kiran na kara wayar a kunnena. “Hello...” “Congratulations an daura aurenmu, Alhamdullahi” Gabana ya fadi har sai da kaina ya sara, kai kace ban tsammaci zuwan wannan ranar ba. “Allah ya ba mu zama lafiya” “Ameen” Ya amsa sannan ya kashe wayar, shi ne mutum na farko da ya fara min albishir, kamin gidan mu ya dauki guda har Hana ta shigo dakin tana rangwada guda tana farinciki, sabanin wacan auren na farko da bata yi farinciki ba. Madadin na yi murna sai na fashe da kuka na zube a gurin an rufe idona ina ta rutsar kuka kamar wanda aka sake yi ma auren dole. Haka na wuni ban iya cin komai ba, sai da Anty Larai ta siyo fura ta dama min ta saka kankara sannan na iya sha shi ma ba da yawa ba, yan'uwan Abdull sun leko mana wuni, daga bangaren mahaifiyarsa da kuma na mahaifina. Angon kuma be duro gidan ba sai isalin karfe takwas na dare. A lokacin da na kira a waya ya sanar min yana waje, sai na jin kunyar fita a dole na yi masa karyar Gwaggonta tace ba zan fito ba. Ban san da wa yayi magana ba, sai ga Baba ya shigo yana fadin na tashi na leka waje mijina ya zo tare da abokinsa yana son magana da ni. Jin cewar yana tare da wani ya karfafa min guiwa kuma ya rage min kunyar da nake ji ta mutane. Hana ta dauko turare ta kara fesa min, Anty Larai kuma ta saka na cire lace din dake jikina na saka farar lafaya sannan na fita gashin kaina na yawo domin ban saka ribbon ba. Nesa da gidanmu ya faka ta inda mutane ba za su ganshi ba, ni ma ba dan na kira shi a waya ba ba zan iya gane shi ba. Kamar ana daure min kafafuwa haka na karasa gurin motar sai ya sauke gilashin ya kunna hasken wayarsa ya haska fuskata. “Amarya ba kya laifi, kyakkyawar amarya mai tsaye siririya duk ni kadai” Kunya ta saka ni sauke kai kasa ina murmushi. “Shigo motar mana, kar na gajiyar da matata” “zan iya tsayuwa a nan” Bude motar yayi ya fito ina kallonsa ya kama hannuna ya zagaya da ni ta baya ya saka ni a back seat sannan shi ma ya shiga. Rabon nake ko zan ga abokinsa amman ban ga kowa ba. “Ka ce kana tare da abokinka...” “Na fadi haka ne saboda na rage miki kunyar dake kanki” Ya yana maganar kallon bakina zuwa kirjina. “Ko ban kyauta ba?” Kamin na amsa na ji na kara matsowa kusa da ni sosai har ina jin numfashinsa, ta dama da ni ya lakamo hannunsa yana lasa cikina a hankali. “Ya gajiyar biki?” “Alhamdullahi” Ina kokarin cire hannunsa sai ya juyo da fuskata zai sumbance ni, na dauke kai na dauke numfashi ina jin wani iri. Murmushi yayi ya saka dayan hannunsa ya juyo da kaina. “Da alama dai kunyar nan zata cutar da ni” Ya sumbanci goshina ya shinshina hancina kamar mai kokarin tantance wani abu. Rufe ido na yi jikina ya hau bari ina jin wani bakon al'amari. Hakan kuma be hana shi kai bakinsa cikin nawa, sai da na ji yana kokarin wuce gona da iri tukuna an matsa baya na rike hannunsa. “Abdull za a iya ganinmu fa” “Babu wanda zai gani bakin gilashi ne” Ya sake kai hannunsa a jikina sai na tare. “Baba zai ga na dade” “Me yasa kike ta guje min ne Noor? Kin san how long nake ta jiran wannan ranar? Ni fa yanxu halalinki ne” “Na sani amman ban tare ba, kuma na fito gida ne da sunan zaka yi magana da ni” “An riga an daura ko da sadakin da na biya kin zama mallakina balle kuma an daura, sadaki shi ne aure ai wasu da zarar an biya sadaki ma suke sakewa juna balle mu da har an daura mana aure” “Auren dai shi ne gaskiya, amman biyan sadaki ba aure ba ne, tun da har ana daura mana ai ya kamata mu yi hakuri har zuwa lokacin da za mu tare babu dadewa” “Allah yasa zan iya jira, sai monday zamu bar garin nan Noor, kuma ba wani abu zan aikata da ke ba a yanzu, it's just a kiss, ina kokarin wayar da ke kamin mu tare domin na lura kamar baki gama fahimtar rayuwa ba” Na yi murmushi karfin ina mamakin yadda yake da rawar jiki haka, kuma ina yaba kokarin Hafiz na jurewa da yayi ashe shi din jarumi ne sosai. Na matsa ta gefen da kofar take na bude na fita. “Sai da safe” “Sai da safe my shy Bride, an hana ni kiss ko? Zan rama” Murmushi na kawai abun da na yi na fara takawa ina tafiya har na isa cikin gidanmu. A dare wata kanwar Mama ta cika min ciki da wasu kayan mata har sai da kaina ya fara ciwo. Haka na kwashe kwana biyu ana ba ni abubuwan nan da bana bukata, ban kuma isa na ce aa sai a rufe ni fada. A cikin kwanakin da na yi a gida bayan daura auren, babu ranar da Abdull baya zuwa da dare a kowa dare kuma sai yayi kokarin taba ni har ya wuce gona da iri. Baba yayi min nasiha da kuma jan kunne, ranar Lahadi Mama ta aiko da mota aka dauki zuwa gidanta ta yi nata nasihar, acan na kwana sai washe gari na dawo. Na dawo gidan na tarar Hana ta gyara min kayana ta kintsa komai, a take na fara jin kewar gidanmu duk kuwa da kasancewar ba wani dadin zaman gidan nake ji na. Ranar Monday da misalin karfe 2pm Abdull ya iso gidanmu tare da wani abokinsa da kanensa mata biyu da sunan za su dauke ni. Sai Baba ya tsayar da shi jege suka tattauna, ban san me suka tattauna a kai ba, bayan sun gama na fito ina sanye da green abaya da mayafinta sai mask da na saka na rufe fuskata. Handbag dina tana hannuna tare da wayata da karamin akwaitin da yace da shi kadai zamu tafi a yanzu saboda jirgi zamu shiga. Yace daga baya zai aiko da mota a dauki saura kayan nawa da kuma yan'uwana domin su ga gurin da muke rayuwa. Da ace ina da iko da tun a yanzu zan tafi da Hana domin ta rage min kewar gida da kuma bakuntar gurin da ban sani ba. Na yi kuka sosai ina jin kamar wata kasar zan tafi ba iya Lagos ba. Har gurin mota Baba ya rako mu tare da Hana da Umma, na shiga gidan baya tare da kanensa shi kuma yayi ma Baba sallama ya shiga front seat kanensa kuma yaja motar sai airport.... Ban taba ganin airport a fili ba sai a ranar da muka isa gurin, ashe babban guri ne mai hada hadar jama'a mun zauna a wani guri jiran jirgin bayan an gama yi mana check-in. Id card din dake hannuna nake ta kallo, sai dai zuciyar da tunanin yana can wani guri. Hannun Abdull na ji cikin nawa yana kokarin saka yatsunsa cikin nawa. “Amarya are you Okay” Na kalleshi sai na ji hannunsa a fuskata yana share min hawayen da ban san taya suka zubo ba. “Har kin fara missing din gida ne?” Ban yi magana ba na kalli kanensa dake can gefe zaune suna ta hirarsu, jira suke har sai jirginmu ya tashi sannan su koma gida. “Ka yi min wani alkawari” “Cewar ba zaka taba cutar da ni ba” “Me yasa kika fadi haka Noor” “Ba komai ni dai ka yi min alkwarin rike ni amana, ina fatan wannan auren da muka yi mutuwa ce kadai zata raba” “In Shaa Allahu, na miki alkawari ba zan taba cutar da ke ba Noor” Ya ba ni tabbacin da nake bukata sannan ya amsa kiran dake shigowa wayarsa ban san da wa yake magana amman na ji yana fada masa lokacin da zamu sauka. Ni kuma na juyar da kaina ina kallon wani gafen. Kalamansa sun saka na ji hankalina ya kwanta, na samu natsuwar da na rasa. Na sani mutum ba zai taba samun abun da yake so dari kan dari ba, shiyasa na yarda da wannan kaddarar kuma na shiryawa wannan zaman aure da dadi babu dadi zan zauna, ko da Abdul zai rika yanka naman jikina ya siyarwa ne. Zan jure ko wace kalar azaba da ukuba ko da kuwa ita ce zata yi silar ajalina... An samu delaying gurin tashin jirgin, karfe biyu da mintuna goma sha biyar ya kamata mu tashi amman ba mu tashi ba sai misalin Karfe uku daidai muka tashi daga filin jirkin saman Aminu Kano, bayan mun yi bankwana da yan'uwan Abdull, har na ji ina ma ace ni ma nawa yan'uwan sun rakoni kamar yadda na shi suka yi. Abdull ne ya saka min belt ya sakawa kasa ya rike hannuna ganin yadda nake jin tsoro sosai lokacin da na yi arba da jirgin for the first time. Sai da muka yi nisa da kasa sosai jirgin ya fara tafiya sannan ya cire min belt din shi ma yhttps://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0 PAID PAGE... ©️KhadeejaCandy ©️®️Copyright 2024 Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba. To be part of the journey pay 500 to 2451879008 ZenithBank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.... You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153 _______•••_______ Abdull ya miko min hannunsa na rika na fita, na yi zaton Zafeer zai wuce ne sai gashi ya fito daga motar ya rufe yana kallon gidan. “Wannan ai zai wadace ku kai da kake ta complain yayi muku karami” Abdull ma ya fara kallon ko'ina. “Ni kam yayi min karami, na fi sha'awar baban gida wannan ai ba zai wuce daukar mota biyu ba” “Haya ce fa, ba gidanka ba ku biyu ne kawai” “Haka zan daure dole mu yi maneji ai, shigo ka ga cikin mana” Kamar zai ce aa sai kuma ya kalleni sai ya fara takawa Abdull ya ja hannuna muna wuce cikin karamin gidan zaman mutum daya. set din kujeru ne falon sai kayan kallo da firjin, kitchen din ma ba wani mai girma ba ne sosai dakin kuma two bedroom ne kawai ko wane da toilet dayan dakin ne kadai yake da gado dayan kuma babu komai a ciki. “Gidan nan yayi datti” Cewar Abdull yana kallon yadda kura ta bata ko'ina. “Sai ku gyara ai” Zafeer ya amsa masa. “Wane irin mu gyara na fa fadawa mai gadin cewar ya gyara mana gidan, bari na dubo shi” Ya saki hannuna ya fice daga falon, sai ya rage daga ni sai Zafeer, hakan ya saka na ji falon ya mana kadan domin har yanzu ina jin kunyarsa, bana son hada ido da shi saboda haka na sauke kaina kasa ina wasa da yatsuna. “Wannan ne aure na biyu ko?” Na dago na kalleshi da sauri. Ashe ya gane ni kuma ya san ni din ce, to me ya fi wannan kunya? Na yi shiru na kasa amsawa. “Haka zaki yi ta yi Noor, har sai kin ji aure ya fita ranki, a lokacin ne zaki gane kin yi ma kanki babbar illa na rabawa zuciyarki da ni saboda kwadayin abun duniya, yanzu ma mai kudin kika sake aure ke dai kokarinki ki gujewa talauci” “Ina ta kokarin na samu damar yi maka bayani Zafeer Wallahi babu..” Be bari na karasa maganar da nake da in'in'in kuka ba ya katse ni. “Damar me? Wane irin roko ne ban miki ba? Wace kalar bibiya ban miki ba? Kin sani son ki jinin jikina ne Noor kin san halin da na shiga da kika juya min baya? Ke da mahaifinki kuka biyewa son zuciya da kudi, kika rufe ido daga ganina Noor, ba ki amsa maganata saboda wasu mutane sun zo daga sama sun nuna miki kudi sai kika ga kamar sun fini daraja, suka raba ni da ke kuma su ba za su iya rikonki ba, haka kuma zaki yi ta aure saboda babu wanda zai iya dake sai ni, babu wanda ya san ki a yadda na sanki Noor... Ni kuma din sun lalata mana komai bana ma son ganin fuskarki” Na share hawayen dake min zuba. “Na san yanzu ka daina so na, amman kana fahimta idan ina maka magana Zafeer..” Nan ma dai be bari na karasa ba. “Da kenan Noor, yanzu kin fado daga zuciya da hannayen da suka rike ki, ko sunanki bana son ji” Na runtse ido ina jin zuciyata na min zafi, yau ni Zafeer yake cewa baya son jin sunana ma. Ina jin takun tafiyarsa ya nufi kofa ya bude ya fita. Bude idanuwana na nufi kujera na zauna na dafe kaina ina kuka, a haka Abdull ya shigo ya same ni sai ya zauna kusa da ni da sauri yana tambayar me ya faru. “Na yi kewar gida, na yi kewar kowa da kowa, na fara jin kadaici tun a yanzu” Ya kwantar da ni jikinsa. “Kukan ya isa haka Noor ko dazun da zaki fito mota da hawaye kika fito, nan da kwanan biyu zaki saba” Na daga mishi kai ina kuka a jikinsa. Sai Magariba muka yi wanka na huce gajiya, ya fita ya nemo wani abun ci, da kuma kaji manya da fura mai dadi irin ta gorar nan da ta sha Nono, sai ice cream da zallar madara mai sanyi. A tare muka ci abincin sai dai ban wani ci sosai ba saboda tunani da damuwa dake kokarin hana ni farinciki a daren farko a gidan sabon mijina. Bayan mun gama na kira Mama muka gaisa ta yi mana maraba da sauka, sannan na kira Baba shi ma muka gaisa. Shi ma ya kira nasa familyn suka gaisa. Safeena ce kira ta karshe da yayi har yayi ya gaji ya aje wayar bata amsa ba. A tare muka yi sallah Isha'i sannan ya saka kayan bachi ni ma na saka muka fito falon muka zauna muna kallo. Dan karkatowa na yi kadan na kalleshi. “A ina ka san mutumen da ya kawo mu dazun?” Ya sosa hancinsa da da hannunsa dake rike da remote. “Zafeer wai?” “Eh” “Ba dade da zuwa gurin da muke aiki ba, matar da ya aura mahaifinta shi ne mai kamfanin, so shi ya turo shi a koya masa wasu abubuwan kuma a nuna masa yadda gurin da ma'aikatan suke, kamin su tashi wuce New York, kuma da ya zo sai ya zama jinina ya fi dahuwa da na shi, cikin kankanen lokaci muka shaku, har baya son na yi tafiya” “Yana da kirki” Na fada ina kwantar da kaina jikinsa. “Yana da shi gaskiya, akwai mutunta mutane, kin ga ai shi ya dauko mu, ko wacan zuwan da na yi shi ya dauko ni Airport, ko na ce ya bar shi sai yace Aa ba komai ba ne, ba wani abun yake yi da na hau taxi kara ya dauko ni” “Amman be taba zuwa gidan nan ba?” “Eh sai yau, ina dai ba shi labari ne a lokacin da na so n samu wani gidan nan canja saboda yanzu mun zama mu biyu ba kamar can da da nake zaune ni kadai ba sai baki idan sun kawo ziyara, wannan kuma ai zaman aure zamu ko?” “Wannan gidan ma ya wadatar, babu matsuwa ai tun da Mu kadai ne” “Haka ne Amaryata” Ya sumbanci hannuna ni kuma na yi murmushin karfin hali. Ina sauraren yadda yake ta aika min sakwannin har sai da ya ji kamar falon ya mana kadan sannan ya kama hannuna muka koma daki. A daren ne na karbi bakuncin Abdull ban hana shi hakkinsa ba saboda ina tsoron kar na sake afkawa a cikin halaka irin na wacan karon. Hakika na ji azaba na ji wani yanayi na dabam, sai dai be kai yadda Aisha ta yi ta koda min a wacan karon da nake farko aure ba. Da gari ya waye sai na rasa ya zan yi domin ni bakuwa ce a lamari na rasa ya zan yi na kula da kaina, bandaki na shiga an rufe na zauna a gurin ina hawayen da a yanzu ban san na minene ba, gaba daya jikina ya mutu. Shi kuma be farka ba sai karfe bakwai na safe. Ina zaune a kasa har zaman ya gundire ina tunanin tashi ya turo kofar dakin yana mika da hamma da alama bachin be wadace shi ba. “My soul me kike yi a nan? Na dauka kina falo ma” “Babu ruwa a bandakin kuma gurin zafi yake min ban san ya zan yi ba” Na fada ba tare da na kalleshi ba. Ya taba fanfo ya murda ruwa be kawo ba. “I'm sorry ina jin sai an tada gen, bari na dora miki ruwa zafi” Sai da ya tada gen din ya dora min ruwan zafi sannan na iya gasa jikina na yi wanka na fito cike da karfin hali. Ganin karfe tara saura na safe ya saka ni cira kafa na dauko hijabina a akwati na gabatar da sallah asuba, a zato ya shiga dayan bandakin ne dake dayan dakin yayi wanka yayi alwala har ya gama sallarsa, ashe yana can kitchen yana hada mana abun karyawa. Ina sallamewa ya shigo dakin, ta madubi nake kallon murmushinsa har ya karaso inda nake zaune, ya rumgume ni ta baya. “My Soul my joy... Shi ne kika yi sallah baki jira ni ba?” “Na yi zaton ka yo sallah ne” “Aa ke nake jiran ki fito ai na shiga bandakin na yi wanka da alwala, ina tsoron na ce zan shiga ki ce zaki ji kunya domin na lura baki son hada ido da ni ma” Ya sake ni ya nufi wayarsa ya duba sannan ya aje ya shiga bandaki yayi wanka ya fito yayi sallah, sai na gaishe shi. “Ina kwana” Ya taso daga inda yake zaune ya dawo kusa da ni ya zauna ya kama hannuna ya rike yana sumbanta. “You drive me crazy my soul, na yi mamakin yadda na same ki kamar baki taba aure ba” Na kara jin kunya ta rufe ni. Ya leki fuskata. “Ko dai baki taba sanin komai ba sai akaina? Ko kuma tsananin gyara ne?” Nan ma ban amsa ba. “Ba zaki amsa min ba?” “Ban taba ba” Ya bude ido sosai irin na mamakin nan. “Mijin da kika aura ba?” Ba tare da tunani ko fargabar komai ba na fada masa irin zaman da na yi a gidan, sai ya cika da mamaki yana ta yaba hakurin Hafiz. “Wannan shi ne garabasa, amman duk da haka gaskiya mutumen da kika aura mai hakuri ne, ni ba zan iya hakuri da wannan ba ko kadan, bana iya daukar wannan” Na masa murmushi kadan ina mamakin idan baya iya hakuri taya yake iya wata hudu, uku a nan kamar yadda ya fada ba tare da matarsa ba. Ko da yake irin wannan hakurin kamawa take na dole ne. Shiyasa ya damu ya kara aure. Akan ce aure dace ne, a yanzu kam ina ganin kamar na dace domin Abdull yana mutunta yana nuna min so da kauna, idan zai fita zan raka shi har gurin motarsa idan ya dawo kuma na tarboshi zai dawo min da tsaraba a kullum haka yake. Girkin ma da ke babu dadi ko ya chabe wani lokacin haka zai ci ko ya siyo wani abu be taba nuna min ransa ya bace ba ko kuma ya rufe ni da fada. Abu daya ne zuwa biyu illar Abdull, shi ne an rashin son ibada, da azuba sai dai na yi sallah na bar shi idan ya farka misalin 8 ko 7 yayi duk yadda zan tashe shi ba zai tashi ba. Na kam lura idan ya dawo daga aiki yana rama sallah azahar kamin yayi La'asar wani lokacin ma sai ya kai magariba yake hadawa yayi, a tsawon zamana da shi ban taba ganin ya bude kur'ane ko da a wayarsa ne ya karanta ba. Sai kuma rashin kishi domin baya son ina saka hijab idan zamu fita shakatawa ko siyen wani abu ko kuma idan abokansa suka zo, yana yawan fada min wai shi yana son abokansa su san wayayin mata yake aure, ya nuna min rayuwar Lagos rayuwa ce da babu ruwan kowa da kowa. Kuma na lura haka din ne, domin idan muka fita ina gani mata da wando ko guntun skirt, ni kuma ina dora hakan ne a mu'auni na banbancin yare, addinin da kuma al'adarmu ba su zama daya ba. Dole hakan ya haifar da banbancin abubuwa dama, amman shi ya kasa gane haka ya dauki rayuwar Lagos ya sakawa kansa kamar ba bahaushe ba. Ba mamaki ta kan iya yiyuwa saboda yawan abokai mata da yake da su ne, yana da females friends da yawa, kuma suna saka kananan kaya wanda kusan ita ce 70% na suturar mutanen garin. Ba illa ba ne idan ya bukaci na saka masa a gida, idan zamu fita sai na saka after dress a sama ko gown. Duk yakin duniyar nan da zan yi ba zai taba yarda na fita da hijab ba, sai dai guntun mayafi kamar wata budurwa. Ko da yake abayar ta kan rufe min jiki, gashi ni kuma din ba mai kiba bace balle na ce ta bayyana surata. Mun sha ziyara har mun gode Allah bokansa sun yi ta kawo mana ziyara sosai, musamman na gurin aikinsu maza da mata, idan za su zo hotel yake tafiya ya siyo abinci, kamar kala biyu ya kawo na zuba a kulolin da ya siya min sabbi domin ban zo da komai ba, sai tufafi su ma atamfa ne sai laces kananan kayan a garin ya siya min su. Ba ni da wata matsala da Abdull sai ta rashin sallah kamar yadda na lura tun farkon zuwana gidan. Ina jin nauyin fada masa kuskurensa gudun kar ya fahimci a abun abaibai, har sai da na fahimci ba shi da niyar gyarawa sannan na fara nuna masa masa muhimmancin sallah da illar da barinta yake kawowa, cikin hikima da dan gutun ilmina. Idan na fadi hadisi ko karatun wasu malamai akan sallah sai na ji ya karasa min, da alama ya san komai ba zahili ba ne, kawai dai shedan yayi nasara a kansa ne ta wannan bangaren. Na kara jajircewa ina tunatar da shi a duk lokacin Sallah ko da kuwa baya gidan. Ya kan dan motsa yayi Sallah a cikin lokacinta wani sa'in, musamman idan weekend ne yana gida tare da ni a tare muke yi. Sai dai a yadda na lura kamar takurawar da nake masa bata masa dadi kawai dai yana min kawaici ne yana yi saboda yana son farincikina. A kwana a tashi hausawa suka ce hasarar mai rai, a haka mu ka kwashe wata uku a gidan, ni kam kadaici ya hana ni na saba da gidan har yanzu, gashi ta inda muke makota na duk yarbawa ne babu wasu kuma ibo ne bana jin yarensu basa jin nawa, sai dai a yadda Abdull ya fada min yawancinsu suna jin turanci, duk da haka dai be amince min na leka gidan kowa ba kullum ina ciki gida kamar kifin gwangwani. Ta wani bangaren kuma ai yana da gaskiya zaman aure na zo ba yawo ba, a yanzu kuma bana bukatar duk wani abu da zai daga hankalin mijina ko rayuwar aurena. A haka na cije na daure na yi zaman da ban tsammaci zan iya ba, a garin da ba ni da kowa sai Allah, sai mijina wanda nake gani a matsayin farincikina a yanzu. Sai da na cika wata uku da sati biyu cif sannan ya yi min izinin tafiya gida domin duba yan'uwa da yan'uwansa. A tare da shi muka tafi ba saboda yanayin aikinsa ba su ba shi izinin tafiya, kuma na lura kamar baya son zuwan ma, zaman garin ya fi masa fadi fiye da Kano a yanzu. Ticket din jirgi ya siya min daga Lagos to Kano, da kansa ya kai ni Airport ya tsaya har sai da jirginmu ya tashi, ina sauka na kira shi na fada masa sai ya turo kanensa ya dauke ni, gidan Safeena aka fara kai ni, wanda zan iya kira da gidan mijinmu a yanzu. Daman ya fada min gidan yake son na fara sauka saboda mu san juna ni da ita. Abun da ya kamata yayi tun kamin mu bar garin be yi ba sai a yanzu. Gida ne mai fadi sosai bangare daya ne a gidan dayan bangaren kuma zallar fili ne da ba a gida komai ba, da alama a nan zai min nawa bangaren idan mun tashi dawowa garin gaba daya. Kanensa ya wuce gaba ya shiga da sallama sai ta amsa masa da karfinta da far'ata. Ina rangada tawa sallamar sai murmushin dake fuskarta ya gushe, waya sani ko be fada mata zan biyo ba, wata kila bata san da zuwan nawa a gidanta ba. Ko ma dai minene oho mata ni ma dai gidan nawa mijin ne bata fi ni iko da gidan ba. Ban jira ta min izini ba na zauna ina kallon falon da aka kawata yayi kyau sosai kamar na sabuwar amarya, hotunan Abdull da yaransa ne suka yi ma falon ado, domin frame ne babba mai wadatar da mai kallonsa. Na fi maida hankali gurin hoton karamin danta da yake kama da Kareem, kuma yake kama da ita, shi kadai ya fita dabam da sauran yan'uwansa dukansu bakake ne kamar mahaifinsu, sai dai farinsa ba mamaki ba ne domin ita ma fara ce. “Duk suna makaranta, Abulkhari kuma bachi yake” Ta amsawa kanenta dake tambayar ina yara. Kamar dai yaron ya ji me ake fada sai ya fara ihu, ta tashi da sauri ta shiga wani daki dake fuskantar dayan ta dauko shi ta fito. Yaro ne dan wata biyar da kwanaki fari sol kamar dai ita, ta zauna a kujera tana rarrashinsa. Sosai nake ganin kamarsa da Kareem, wata kila dai saboda na san alakar da ta taba shiga tsakaninsu ne zuciya yake raya min abun da be dace ba kuma bana fatan ya faru. “Amarya ya angon na ki?” Na dago daga tsananin kallon da nake yi ma danta na kalleta. “Lafiya kalau muke, ya muka same ku?” “Muna cikin aminci da kwanciyar hankali” Ta amsa min fuska babu annuri tana min kallon biri ina mata kallon bishiyar hawa. “Dawood a kawo maka abinci?” Ta tambaye shi kadai ba tare da ni ba. “Aa ni wuce zan yi sai dai kanwarki idan zata ci” “Kanwata tana gidanmu tana taya iyayena aiki, kanwata ai ba zata aure min miji ba, kuma ta ne mi daga min hankali” “Idan har ni na daga miki hankali, to daman can cikin tashin hankalin kike na abun da yake boye a zuciyarki, ni kan aurena sai dai ya haifar muku da kwanciyar hankali ke da mijinki” Na bata amsa daidai da furucinta. Dawood ya mike tsaye “Miye wannan abun dan Allah? Ku da za ku hada kai ku kwantar masa da hankali, cewa fa yayi na kawo ta ku gaisa miye na wasu kananan magana dan Allah? Haba” “Har a bada ba zan hada kai da macijiya ba, ki sare ni a gaba ki sare ni a baya kuma ki yi sammanin hada kai da ni, ai kin yi shuka ne a idon makurwa, shi dai da ya ji zai iya da yaje can yayi ta yi, ma san abun da maza suke gani a jikinki da suke rawar jiki, abu kamar daurawa muciya zane” Na yi murmushi kai kace ban ji zafin maganar da ta jefa min ba. “Abun da baki da shi, shi suke hangowa” Sannan na mike tsaye ina tabe baki. “Ni ba fada ya kawo ni ba, mijina yace na biyo na gaishe da matar kuma na cika umarni, kin san ni ban iya cin amanar miji, Malama kin ga tafiyata” Har na juya sai kuma na juyo na kalli yaron dake hannunta. “Allah ya yara abulkhari yayi masa albarka, sauran yaran kuma idan sun dawo a ce new Momynsu tana gaishe su” Ta aje yaron ta mike tsaye a lokacin da Dawoo ya kai kofa ya bude min yana fadin na zo mu wuce. “Karya kike yi Wallahi har gobe yarana ba su da wata uwar sai Safeena, wato ku yan matan zamani yan matan titi da suka gama ganin duniya aka gama da su, shi ne kike son shigowa cikin gidana ki mallake gidan ko? To kin yi kadan” Na yi murmushi mai sauti. “Ashe dai kina son mijinki, to ki tana a hannu karki nemi daga min hankali domin kilu zata iya kan bau. And for your own information ni ba malleke gidan nake son yi ba, nawa ginin nake ginawa sabo fillll” Zancen kilu ta ja bau ya saka ta saranda, bata sake yunkurin furta wani abu ba har na bar falon, a mota kanensa yake ta yi min nasiha wai sai na yi hakuri kishi ne yake damunta har yanzu, ya san halin matar yayanshi da tsananin kishi. Har muka isa gidanmu ban daina jin zafin magangunta ba, musamman da tace min kamar an daurawa muciya zane. #KhadeejaCandyhttps://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0 Can cikin bachi na ji ya taba an taba ni, hakan ya saka ni bude ido sai na ga wutar dakin a kunne. “Taso mu yi magana” Ya riko ni na tashi zaune ina sanye da kayan bachi wando ne da ya tsaya oya cinyata dai karamar riga marar hannu. Shi kuma yana sanye da pajamas dark green. “Me ya faru?” Na murza ido. Ajiyar zuciya ya sauke ya kama hannuna ya rike. “Noor ina son ki fahimce ni please, ba wai bana son haihuwa ba ne kawa...” “Indai maganar zubar da ciki ne, zai fi maka kyau ka tafi ka kwanta, ba zan zubar ba Abdull” Ya kara sassauta muryarsa alamar rarrashi. “Baki gane ba, ni gani nake ma kamar ba zaki iya haihuwa ba, kalli kunkurunki ma fa, karami ne sosai kuma be kamata ki fara haihuwa da kurciyarki kamar haka ba, Safeena ma sai da muka yi shekara biyu tukuna ta fara haihuwa...” “Babu wasu kalamai da zaka iya daure ni da su Abdull, ni dai kawai abun da zan roke ka ka aje sirrin nan a tsakaninmu, bana son yar'uwata ta san mijina ya juya min baya, kuma bana son ta san baka son abun da zan haifa, mu kwana lafiya” Na juya na kwanta na ja bargo na lulluba har kaina. Kwafa na ji yayi ya tashi ya fice ba tare da ya kashe min wutar dakin da ya tarar a kashe ba. Tashi na yi zaune na ina hawaye. Daren be mini dadi ba saboda haka ban runsa ba. Sai bayan na gama sallah na kishingida jikin gadon dake dakin sannan bachi ya dauke ni kadan, domin ban dade ba na farka saboda kiran da yake ta kwala min kamar zai tashi gidan. Na zabura na fito falon ina kallonsa. “Karfe Nawa ace baki hada abun karyawa ba? Ko salon na yi magana ki ce layi kike ke ga mai ciki” “Zan shiga na hada yanzu” Ita ce amsar da na bashi sannan na cire hijabina na aje akan kujera na shiga kitchen na fara dora ruwan zafi, ina tsaka da soya kwai amai ya taso min domin bana son karnin kwai a yanzu. Da gudu na fito na shiga bandaki na yi amai na wanke bakina da hannuna da fuska sannan na fito na shiga ba da aikina. Sai da na gama hada masa komai na kawo a dinning na aje sannan na koma kitchen din na gyara shi. Na fito cike da gajiya sai na ganshi da shirinsa na fita. Kallon mamaki na yi masa kamin na yi magana ya ce. “Ba zan iya cin wannan breakfast din na kazanta ba, sai ki zauna ki ci” Wani bakincikin ne na ji ya ratsani, yanzu ya san ba zai ci ba kuma ya saka na girka? Ai ya sani dole zan yi amai me yasa be girka da kansa ba? Da kallo na bishi har sai da ya kai kofa sannan ya juyo ya kalleni ya ga har lokacin kallonsa nake na ma kasa motsawa daga inda nake tsaye. “Barakallah Maa Shaa Allah, babu abun da zaki iya yi da ni, idonki ko mugun nufinki a zuciya ba zai min komai ba, na sha tabara na sha yasin nan gani nan bari Abdullahi kam, duk wani nufin da kike da shi akaina sai dai ya koma kanki lafiya zan tafi lafiya zan dawo kuma lafiya zan cigaba da rayuwata” Ban san lokacin da hawaye ya zubo daga idona ba. Shi kuma ya bude kofar ya fita ya bar ni rumgume da bakinciki. A gurin na zauna ina tambayar rayuwa me yasa take min haka? Ina tunanin kamar na dace sai kuma wannan ya bullo min? Kamar an karfafa min guiwa haka na ji sai na mike ina fadawa kaina cewar zan iya jure wannan ma kara bakincikin gidan miji da wanda zan fuskanta a gidanmu ko unguwarmu. Dakina na shiga ina gyarawa ina mamakin wai haka Safeena take rayuwa da shi idan yana kusa da ita ko kuma dai ni yake yi ma haka saboda baya son haihuwa? Wata kila shiyasa take son Kareem sosai take ta rufe ido tana aikata abun da zuciyarta take so. Waya sani ko ita ma bata jindadin zama da shi. Na yi zaton shi zai aika mata da kudin mota ko ya siya mata ticket din jirgi ta zo ta jirgi amman be yi ko daya ba. Dan kudin da nake samun gunsa ne lokacin da yake so na na hada na bawa Mai gadi ya saka mata a pos ta account din mai pos din unguwarmu. Sannan na fada mata ta rubuta number wayata a takardar saboda idan ta iso ta ari wayar wani ta kira sai a na fada mata inda za a kawo ta. Sanin dakuna biyu ne a gidan ya saka na kwshe kayan Abdull da suke dayan dakin na dawo da su dakina kamar yadda suke a da, domin ba zan kwana da ita a dakina ba shi kuma ya kwana a daki daya dabam, hakan ma be dace ba, kuma zata iya fahimtar kamar ba ma zaman lafiya tsakaninmu. Ana gobe zata taso sai gashi ta kira ni da bakuwar number ta fada min karamar waya ce Mama ta bata tare da layi a ciki, kuma ta kara mata wani kudin da zata rike saboda expensive na hanya. Na jidadi sosai hakan zai taimaka mu rika communication kamin ta iso. Washe gari misalin 6am na kirata domin ta fada min tun asuba zata tafi ta sha. Duk bayan awa daya sai na kira ta fada min yanzu suna guri kaza da haka dai har suka sauka Lagos. Na fada mata sunan unguwarmu ta tari okada ta hau, a nan sai da aka kara bata lokaci saboda yamma ta yi, akwai cinkoson mutane sosai. Ina jin an taba gate na fito daga falon da sauri na, a lokacin da muka hango juna ni da ita sai murna ta bare na je gurinta a guje ita ma ta yo kaina a guje ta bar jakar kayanta a gurin tana murna. Tsalle nake ina direwa tsabar murna da jindadi na ga yar'uwata, domin na san abubuwa za su zo min da sauki. Mai gadinmu ne ya riko jakarta ya shigo da ita cikin falo, sannan mu ma muka shiga ina tambayarta ina Mama ina Baba. Sai da ta huta na kawo mata indomie da na dafa ta ci sannan take ba ni labarin yadda aka yi ta rigima kamin Umma ta amince mata ta zo saboda ganin take idan Hana ta zo sana'ar da take zata gurgunta babu mai fitar mata da awara. Abdull be dawo gidan ba sai misalin 10 na dare, ina zaune falo ina kallo ya shigo fuska babu annuri, a lokacin Hana ta yi bachi a dakin da na nuna mata zata rika kwana. “Sannu da zuwa” Yayi kamar be ji ba ya nufi dakin. “Hana tana ciki na maida kayanka a dakina tare zamu rika kwana har sai ta tafi” Ya juyo ya kalleni. “Saboda kin raina ni ko saboda me? Vabu sanarwa babu komai zaki kwashe kayana ki kai can, kuma ki aje ta nan?” “Amman dai ai ba falo zata kwana ba? Kuma zai yiyu na kwana da ita daki daya ba alhalin kana mijina, na fada maka bana son kowa ya san zaman da muke yi, amman idan haka ya bata maka rai ka yi hakuri” Guntun tsaki yaja ya wuce dakina ba dan ransa ya so ba. “Allah ka ga halin da nake ciki, Allah ka shirya min mijina ka karkato da shi ya fuskance ni” Na yi addu'a na shafa sannan na mike tsaye na bi bayansa. Washe gari ma be ci abun da na girka na breakfast ba saboda ni na girka, Hana tana daki tana ta bachin gajiya bata farka ba sai 11am a lokacin Abdull ya dade da barin gidan. Tsintsiyar dake hannuna ta karba. “Kawo na share miki ba dan halinki ba” Na kai mata dudu a baya daman ta fini naman jiki, ni babu komai a jikina sai kashi ba kamar ita ba da take da cikar gaba da jiki, wasu har cewa suke ma ni ce kanwa ita ce Yaya. Ta share gidan tass ta gyara ko'ina sannan ta dora mana girkin rana bayan ta gama cin nata breakfast din. A nan ma mun sha hira har Mama ta kira a waya muka gaisa, na kira Baba muka gaisa sannan ya fada min Hana ba zata dade a gidanmu ba, da zarar na fara jin sauki zata dawo, a haka din ma na yi masa godiya domin yayi kokari da ya barta ta zo ma. A ranar ma Hana bata ga Abdull ba, washe gari ma ko da ta tashi ya tafi aiki, har take tambayar su basa samun sukuni ne tun safe suke fita kuma basa dawowa sai dare yayi sosai, na yi mata karya da cewar yanayin aikin ne yanxu a haka. Sai da ta kwashe kwana biyu a gidan sai a rana ta uku suka hadu kasancewar weekend ne, babu aiki kuma ita take girma mana abun karyawa a yanzu, na jidadin ganinta da yayi burina ya fahimci ba ni nake girkin ba a yanzu ya rika ci saboda kar yar'uwata ta zargi wani abu. Sun gaisa cikin mutunci yayi mata ya gida ya mutanen gidan duk ta amsa da lafiyarsu kalau. A ranar ni da ita da shi duk a dinning muka yi breakfast ina ta Jefa masa hira sai ya ga dama yake amsawa, arziki na daya be fadi wata maganar marar dadi ba, har muka gama. Sai da zai tashi yake tambayar wa zai girka abinci a yau. “Hana zata girka ai ita take girkawa a kullum yanzu” “Me za a girka?” “Me kake so?” Na tambaye shi sai ya kalleta. “Kin iya dambu?” “Babu abincin da Hana bata iya ba, ta fi ni kokari ita bata jin wahalar aiki da girki ma” “Sai na ci na ji zan tabbatar” Ya amsa ba yabo ba fallasa, kamar dai bakar magana kuma kamar a bakin gaskiyarsa kenan. Na yi murmushi “Shikenan sai ta baka mamaki kuwa” Ya kalleta kadan ya dauke kai. “Za mu gani” Na yi dariya ita kuma ta yi murmushi. Sai da ya bar dinning sannan take fada min next time zata zuba nata abincin ta ci a dakinta. “Why?” “Ni dai kawai na fi jin sakewa, ki bar ni na ci a dakina ku kuma ku ci a falo” “Shikenan ba dole ai sai rai na so” Na fada mata ina dariya. Ya ci abun da ya girka da rana saboda a gida ya wuni, be yaba ba amman kuma be isa yace be yi dadi ba domin kowa ya ci dambu a ranar ya san yayi dadi. Da haka dai har ya gaji ya fara yabawa idan ta yi girki, wani lokacin har cewa yake a sake yin jiyar jiya. Sannu a hankali ya fara sakewa da ita ita ta dan sake da shi har sukan zauna su yi hira a falo. A gaba ranar yake tambayar makaranta ta fada masa ta kare amman bata cigaba gaba ba saboda tana jin Baba ba zai aminta ba. “Indai haka ne sai mu rike ki a nan a saka ki a makaranta, ga makarantu masu kyau a nan, kuma da ganinki zaki yi kokari ba kamar Noor ba” Na kalleshi da sauri ina hade rai irin na wasa, jin yana shigar mata a yau, domin idan yana wasa da ita nuna yake na fita iya komai alhalin ya san kuma ta fi ni. “Yau kuma?” Yayi saurin kai hannu ya taba ni. “Ke wasa nake, ta ina zata fi Mamata kokari, kawai ina dan zuga ta ne kar ta ji babu dadi” Muka yi dariya dukanmu. After magariba ya fita titi zagayawa, ni kuma na yi dawo falon na zauna inda Hana take cin abinci. “Noor gaskiya yanzu kam kin dace, yadda kuke rayuwa da Abdull abun ya burgeni Allah yasa hakan ya dore” “Ameen” Na amsa ina hamma, domin tun da na shiga wata na hudu nake ta yawan bachin dare, da zarar an yi magariba zan fara jin bachi sosai. Sai bayan sallah isha'i ya dawo tare da tsarabar suya. Hana ta dauko katon plate aka zube kamin kowa ya kai hannu ni har na kai baki tare da albasa da tumatir. Sai da ya ci yanka biyu sannan ya kalli Hana ya ce. “Ci mana” Sai ta mike tsaye. “Bari na dauko plate a saka min” “Kamar ya? Ki saka hannu mu ci a tare, hana karki zama bakauya yar zaria mana” Muka kwashe da dariya daman kowa ya san yan zaria bayin kanawa ne. “Ni dai zan fi jindadi na ci ni kadai” “Wallahi ba zan zuba ba, idan ba zaki zo ki saka hannu mu ci tare ba sai dai ki hakura ci” Jin yayi rantsuwa cikin zafin rai ya saka ni ma na yi mata magana sai ta dawo fa zauna ta saka hannu muka fara ci a tare dukanmu, har hira ta biyo baya yana fada min gurin wani basakkwacce mutumen yabo ya siyo suyar nan. A take kuwa Hana ta saka santi. “Har na tuna da wani kilishi da Mama ta ba ni da naje mata bankwana tace daga Sokoto aka zo da shi a local government Dange, Dangin kilishi” Muka saka dariya har sai da na sarke, ita kanta sai daga baya ta gane santi ta yi. Na jidadin yadda Abdull yake kula Hana, da farko na yi zaton wulakanci ne zai biyo bayan zuwanta gidan, sai gashi har da ni ya canja min na samu sassauci, na yadda yake mu'amala da ni daga samun cikin. Sai dai kuma a duk tsawon lokacin Abdull baya kai hannunsa balle jikinsa a nawa, zamu kwana a gado daya mu tashi amman ba zai ma bari ko a kafadarsa na kwanta ba. Na yi masa uzurin wannan saboda na san baya son cikin, wata kila yana hora ni ne har yanzu. Ta dayan bangaren kuma bana mamakin kaurace min da yayi, musamman a yan kwanakin nan da nake yawan farkawa tsakar dare na ga baya nan amman ina jin motsin ruwa a bandaki, wata kila yana biyawa kansa b*ka*ta ne saboda ya kaurace min gaba daya. Ranar da Hana da cika wata biyu da sati biyu a gidan ta fara min zancen komawarta gida, saboda Baba ya matsa ta dawo, kullum ya kira waya fada yake mata, bata dawo ba. Sai tace masa ban ji sauki ba, da muka kai shi makura sai ya rufe mu da masifa daga ni da har ita yana ta zaginmu a waya. Washe gari friday kamar kowace jumma'a ya shirya cikin manya kaya na malam bahaushe yana ta kamshi, yana tsaka da saka agogo na ce. “My Soul jiya Hana ta yi min zacen tafiya gida” Ya juyo ya kalleni. “Tafiya gida kamar ya?” “Gida dai wai tana son ta koma saboda na fara jin sauki, kuma Baba ma ya matsa gaskiya Saboda Umma take yi ma sana'a” “Aa ba yanzu ba, ta bari sai kin haihu tukuna, idan zaki koma gida sai ku koma tare, ko ma ku yi zamanku a nan gaba daya” “Baba ba zai yarda ba, yayi ta mana fada jiya fa sosai saboda dawowarta, wai taje ta zauna” “Toh wai idan ta koma me zata masa ne?” “Babu fa kawai tana yi ma Umma talla ne ina tunanin Umma ke zugawa ta dawo, saboda sana'arta” “Ki yi magana da ita ta yi hakuri ta zauna a har sai kin isa haihuwa mana” Zan yi magana ya riga “Bari na yi mata magana” Ya juya ya fita, sai na sauka daga kan gadon na bi bayansa. A falo muka same ta zaune tana rike da remote. Abdull ya fara mata magana sai ta nuna masa ita bata da matsalar zama, matsalar ta Baba ce sai ya aminta. “Fada min gaskiya ko dai saurayinki ne ya matsa ki dawo” “Hana bata da saurayi for now” Na amsa sai ya wara ido yana tsokanarta. “Taya tsaleliyar budurwa irinki, ace bata da saurayi duk kyaun nan na ki” Ta rufe ido tana jin kunya. Sai yayi murmushi ya ce. “Zan kira shi na yi magana da shi, wata kila yana jin nauyi na ne shiyasa be taba kirana yayi min magana ba, idan ma ta kama na rika saka masa wani abu a account da za a rika bawa Umma madadin kudin tallarki zan yi haka, daga nan ma sai ya aiko mana da takardunki a sama miki makaranta ki samu ko nce ko diploma” Ni da ita muka kwalo ido waje ta taso da gudu ta rumgume tana tsalle tana murna, ta duka kasa tana masa godiya. Ni ma na masa godiyar ina jin kamar Allah ya amsa addu'a ta ne ya sauya masa yar rayuwar da ya fara na wulakanta. Domin kyautatawa yar'uwa ta jini kamar kyautata min ne. Be ce komai ba sai kallonta yake yana murmushi har ta dauki karamar wayarta ta kira Mama ta shiga dakinta tana fada mata. “Kanwarki ta fi ki kyau Noor, ko wani friend dina da ya zo ranar ya ganta sai da yace yana da kyau” Ya fada min kai tsaye, ba tare da fargabar komai ba na yi murmushi, ai jindadi ne a yabawa dan'uwanka a gabanka. “Tana da kyau, kuma ita tana da jiki ba kamar ba” Ya mike tsaye yana lalaba aljihunsa. “Ba wani jiki da ita sosai ba, ta dai fiki cika ne kawai. Zan tafi sai na dawo” “Allah ya tsare, ka siyo min rake idan zaka dawo” “Toh” Na raka shi har waje sannan na dawo cikin gidan. Ina jin hana tana ihu da murna kamar zata fasa gidan dan murna, na zauna kan kujera ina murmushi yau kuma ta zama kamar ni da hauka. Kamar jira ake na zauna sai na dan abun da ke cikina yayi motsi, ban taba ji ba sai ranar na bude rigar da sauri na kalli cikin, sai ya sake yin motsi da sauri. Hawayen farinciki ya cika idona na kai hannu na shafa cikin ina jin sanyi a cikin raina. It's 500 Zenith Bank Hadiza Abubakar 2451879008 And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0 KAREEM POV. Dagowa yayi daga rubutun da yake a diary ya kalli Safeena dake zaune gabansa fuska a murtuke kamar an mata mutuwa. “I thought na fada maki bana bukatar sake ganinki?” A take ta yi murmushi. “Ta ina zaka so ganina ka samu sabuwar mace? Ka ba ni mamaki Kareem, ashe zaka iya bude zuciyarka wata ta shiga not just zuciyarka jikinka ma zaka iya hadawa da ita?” “For the very last time ko ki fita ko na saka security su fitar da ke” Wannan karon dariya ta yi. “Ashe zaka iya wulakanta ni saboda wata banzar bazara, me ta fi kwarewa akai? Karamar yarinyar kamar Noor zata dauke maka hankali” “Karki sake zaginta, tana gidan mijinki tana zaman aure noor ba karuwa ba ce, ta san mutumcin aurenta” Ta runtse ido kadan ta tauna halshenta. “Ni da kai ne ba mu san darajar aure ba kenan? Da rarrashi na zo gurin amman na lura gaba daya ta canja maka tunani akaina ta canja maka kwakwalwa, shikenan” Ta mike tsaye. “Daman na zo nan ne na ji, cikin dake jikinta na mijina ne ko naka?” Kareem ya watsa mata wani mugun kallo. “Ita fa ba fasika ba ce” “Kawai dai na tambaya ne, saboda na sani kamar yadda ita ma ta san cewa dan da na haifa yanzu naka ne” Ya kalleta without blinking try to connect his heart with his brain. “You're stupid...” Ta yi murmushi “Yau har na kai haka? Lallai Kareem kai ba dan goyo ba ne, cikin kanen lokaci ka canja min, gaba daya yarinyar nan ta dauke maka hankali, haka mijina yanzu ba shi da lokaci na” “Daman mijinki be taba lokacinki ba, dan haka karki zargi Noor, idan ya koma garin da yake manta ki yake yana can yana sha'aninsa kina na ki” “Muna na mu dai” Ta gyara masa tana kallon idonsa cikin bakin rai. “Me yarinyar nan ta tare miki ne wai? Baki da magana sai na ta” Ta zagayo Inda yake yana ganin hakan ya mike tsaye. “saboda ita ta kwace min kai, a rayuwa kai ne kadai mutumen da zaka nesanta da ni, azabar son ka ta azabtar da ni na kasa hakuri da kai, da ba haka kake ba, amman zuwan yarinyar gaba daya ka sauya min kuma ka kwashe sirrinmu gaba daya ka fada mata, har tana yakata da shi, baka jin kunyar mu'alama da mata har biyu? Bayan karyar da ka yi min akan Yusura?” “Ban taba hada shimfida da Noor ba, kuma ba zan taba ba har abada, indai har sai ta kazantacciyar hanya zan samu Noor, to ina rokon Allah ya hana min ita har abada, kuma aure take a yanzu bana fatan ya mutu, fatana ta samu kwanciyar hankali a ko'ina zata kasancewa?” Ta dan matsa baya. “Baka taba kaiwa jikinta ba? To me ya dauke hankalinka ka fada mata sirrinmu? Ba na mu'alama kadai ba wai har na haihuwar da muka yi?” “What? You're not serious? Taya za fada mata abun da ba ayi ba?” Ta matso kusa da shi tana kallon wayar idonsa. “Miye ba a ayi ba a ciki? Haihuwa ko alaka?” “Na ji na fada mata alaka, amman yaushe muka haihuwa balle na fada mata?” “Yanzu kuma kokarin wasa kake da hankalina?” “Wane irin wasa da hankali? Karya kika mata cewar mun haihu ne? Idan ma kin yi haka to kin yi akan aurenki ne kina kashe kanki ne, domin Noor baki ba linzami ce” Ta kalli gefe sannan ta sake kallonsa. “Taya zan fada mata sirrina? Kai ka fada mata, shiyasa da ta zo gidana ta fada min magana son ranta” Ya fisgota ya rike cinyar hannunta. “Stop talking about Noor, yaushe muk haihu? Are you out of your mind?” Ta fisge hannunta. “Ai na fada maka tun ina da ciki ko? A asibitin nan aka karbi haihuwa danka, kuma Wallahi jininka ne! Au kenan baka yarda ba da na fada maka? Ka dauka karya nake?” Kareem ya daka mata tsawa. “Yaushe rabon da na yi wani abu da ke? Akwai dai abun da kike kokarin yi Safeena” “Babu abun da nake kokarin yi, ni ba zan iya cutar da kai ba, amman ďan da na haifa yanzu Wallahi naka ne, last haduwar da muka yi na samu cikin, sati biyu na kara akan lokacin da nake period a satin Abdull ya dawo, yana barin garin nan naje aka min test aka ce ina da ciki dan sati uku, yaron da na haifa yanzu idan aka kalleshi kallon kurilla za a san cewar danka ne, idan baka yarda zan kawo shi ka gwada jininsa” He lost his temper when he was saying. “Baki da hankali Safeena? Taya zaki aje ciki i mean taya zaki haihu? Dan Haram ne Safeena kuma ki dauka ki kawai mijinki? Ina da aure da yaya safeena kina da aure da yaya taya zaki yi haka?” Ya fadi zaune yana rufe bakinsa. “I don't believe you?” “Na kawo maka yaron ka auna?” Ya kalleta. “Idan gaskiya me ye hujjarki na aikata haka?” Ta risina a gabansa. “So so ne, Kareem ina kaunarka ba zan iya zubarwa ba, ko da ba zan same ka ba zan so aje jininka, kuma waya sani ko nan gaba mu kasance ma'aurata” “Ina zamu kai zunubin Safeena? Ga na zina ga na daukar alhaki? Mu dauki alhakin yaron mu dauki na mijinki? Why how? Why why why Safeena why?” “Ni ma bayan na haihu na yi tunanin be kamata mu yi haka ba, amman komai ai ya riga da ya faru, kuma ba a kanmu farau ba, suna nan da yawa yaran da ba na iyayensu ba” Ya kalleta babu alamar wasa ya ce. “Je ki dauko yaron” Ta mike tsaye ta dauki jakarta ta fice daga office din. Fuskarsa ya shafa yana jin gumi na karyo masa, daman da ta fada masa tana dauke da cikinsa gaskiya ta fada? Ya dauka tana masa wasa ne ko barazana shiyasa ta dawo asibitin. Kuma tun bayan rabuwa da ita be sake bincikarta komai ba saboda yana tunanin ya yanke alaka da ita. Ya mike tsaye yana jin kamar baya iya numfashi. “I can't believe this ba gaskiya ba ne, Kareem” Ya fadawa kansa yana nufar windows din ya rika gaba daya ya rasa me ke masa dadi. Juyowa yayi da karfi ya dauki keys dinsa ya fice daga restaurant din gaba daya. Gurin aikinsa ya koma, ya kira waya ya sanar mata inda yake, a can Safeena ta kai masa yaron mai cike da koshin lafiya mai jiki da haske gwanin sha'awa. Tun da Safeena ta aje yaron yana kallonsa gabansa na faduwa domin ya ga kamaninsa a fuskar yaron, ta dayan gefen kuma yana kama da Safeena. Be ce mata komai ya fita office din, babu jiwa ya dawo sanye da safar hannu ya debi jinin yaron a syringe. “Idan har abun da kika fada ya tabbata Safeena kin cutar da ni, kin cutar da kanki kuma kin cutar da yaron nan” Ta kalli yadda yake kuka bayan Kareem ya dauki jininsa ta ce. “Abu ne da zamu iya ajewa, mijina be sani ba, matarka bata sani ba, to mu bar shi a boye mana, sirrinmu ne ai” Be sake ce mata komai ba ya fice daga office din. Tun tana jiran dawowarsa har ta gaji ta tashi ta fita. Be bar asibitin ba sai da ya debi nashi ya hada ya kai laboratory suka auna masa. He wait they sai da aka hada results aka ba shi. Tsoron abun da zai gani ya saka shi kasa duba takardar har ya shiga motarsa. Ta zauna a motar na tsawon awa daya yana tunanin yadda rayuwa zata kasance masa a yanzu, idan har ta tabbata dansa ne, idan a gurin wasu ba abun kunya ba ne shi a gurinsa abun kunya ne. Daker ya ja motar ya fice daga asibitin, be yi nisa ba ya faka gefe titi ya kai hannu ya dauki result din ya duba. Booom..... Zuciyarsa ta buga da karfi, gaskiya Safeena ta fada, dansa ne jininsa ne. “Why Safeena Why?” Na hade takardar da karfi ya yaga ya jefar ya bugu sitiyarin motar da karfi, ya bude motar ya fita ya fara tafiya sai kuma ya juyo ya dawo ya halbi motar da kafarsa. Ya jingina ya rufe ido ya zai yi? Me yasa ya aikata tun farko? Yaya kenan yanzu? Ya bude motar ya shiga ya kwantar da kujerar motar ya kwanta ya rufe ido. Be daga ba sai da lokacin sallah magariba yayi, a wani masallaci dake kusa da gurin yayi sallah Magariba ya kasa fitowa masallacin har aka yi sallah Isha'i. Sai kusan Tara da rabi ya doshi gidansa. Yana driving yana jin kamar kar ya tafi, kunya hada ido da iyalinsa yake duk kuwa da kasancewar ba su san komai akai ba. Harabar gidan ya faka ya kwanta a motar ba bachi yake ba tunanin yadda zai tafi da wasu abubuwa yake. Yana tuna shawarwarin da abokinsa ya ba shi lokacin da yake raye. Da kuma yadda zuciya ta debi shi ta saka idonsa ya rufe a lokacin ya kasa fahimtar illar da Zina zata yi a rayuwarsa. Ya sani duk wani abu da Allah yace kar a kusance shi, ba abu ne mai kyau ba. Ba ma karku aikata ba kar ma kusanci inda take balle har ku aikata haka Allah ya fada, amman ya take sanin ya murje ido ya aikata, yanzu wa gari ya waya? Kamar zai fadi haka ya bude motar ya fito jikinsa babu kuzari. Sai da ya daga kansa sama ya kalli gidan gabas da yamma sannan ya taka ya isa bakin kofar falon ya shiga. A hankali yake takawa har ya haura sama, dakin yaransa ya fara turawa sai ya samu suna bachi an kashe wutar dakin an kunna musu ocean, sakin kofar yayi ya shiga cikin dakin dakin ya zauna kusa akan gadon Tine yana kallonta kamin ya juya ya kalli Areef. “Maybe nan gaba ku ji kun tsane ni, idan ina raye ko a mace, ku yi bakinciki da na kasance ubanku, kuna da yancin yin haka, domin na bar muku abun kunya, bayan ni kuma nawa iyayen ba su bar min abun kunya ba, sun yi kokarin tsare mutuncinsu da na mu” Ya hade yawu. “Ni dai na san ba zan kashe yaron nan ba, duk wani abun da zan biyo baya dole na karbe shi domin ni na aikata, but no matter what ku sani ina matukar kaunarku kuma ina kokarin na tsare mutuncinku, saboda kar na lalata Future dinku” Ya shafa kan Tine ya sumbance ta, sannan ya tashi ya nufi dayan ma ya shafa kansa ya sumbance shi, ya kallesu cike da bakinciki sannan ya fice daga dakin ya ja musu kofa. Dakinsa ya shiga, yadda ya shigo sanye da talkami da kananan kaya haka ya fada saman gadonsa ya rufe ido, ko agogonsa be iya cirewa ba. Haka ya kwanta har safe ko kadan be yi bachi ba, sai juyi yake idan ya gaji da kwanciyar sai ya sauko kasa ya zauna. Sai da asuba ya siya motsawa ya cire tufafin jikinsa da talkamin ya shiga bandaki yayi wanka tare da alwala ya shimfida carpet, nafila ya fara yi sannan ya gabatar da farilla. A lokacin da ya daga hannunsa zai roki Allah sai kunya ta kama shi, ba zai iya komai ba sai kuka, to me zai ce Allah yayi masa bayan ya bijirewa umarninsa ya bi son zuciyarsa? Allah ya hana shi kuma ya aikata, yanzu kuma ya roki me? Mafita? Ko yafiya? Shafa hannayensa yayi a fuskarsa ya kwanta a gurin feeling so hopeless. Kansa har wani nauyi yayi tsabar damuwa da fargaba da suka same shi lokaci daya, ga kuma rashin bachin da be yi ba gaba daya daren jiya. Usually yaransa suna tafiya makaranta ne ba tare da jiran su ganshi ba, wani lokacin ko da za su tafi yana bachi, Yusura kuma ta koya musu idan yana bachi basa tashinsa. But yau sai ya sha banban da sauran ranakun, Areef ya fara shigowa rike da jakar abincinsa Tine na bayansa, Kareem na jin motsinsu sai ya rufe idonsa not like he don't want to see their faces but kunyar kallonsu yake kuma bakinciki zai taso masa ne. “Bachi yake Areef mu tafi” Areef be ji maganar yayarsa ba sai da ya leka fuskar mahaifinsa ya ga da gaske bachin yake sannan ya juya suka yafi. Suna fita Kareem ya bude idonsa yana kallon ceiling da raunannin idanuwansa. Ya tashi zaune, ya dafe kansa, gaba daya ganin yake kamar ranar jiya ba gaskiya bace mafarki ne. Misalin tara ya shirya cikin kananan kayan babu zancen saka agogo ko shafa mai turare da ya zame masa dole kawai ya tsaya domin baya iya rayuwa babu kamshi. Gefen gadonsa ya zauna ya bude drawersa ya dauko diary da pen yayi rubutu a kai ya nade ya aje pen din ya mike tsaye ya dauki wayarsa ya fice daga dakin. Da dai daya ya rika taka stairs din yana saukowa yana kallon Yusura dake goge dinning kanta babu dankwali. Damuwa ta bayyana karara a fuskarsa kyawawan idanuwansa sun fada sun yi ja sosai irin na wanda be ga bachi ba bachi be ganshi ba. Kusa da ita ya karasa ya aje mata takardar a dinning. For the first time ever ta ji gabanta ya fadi irin faduwar da be taba ba. Ta kalli takardar ta kalleshi. “Miye a ciki?” Ya kalleta. “Yancinki ne, yancin da kika dade kina nema” Ta hade abu da karfi. “Babu amfani Daddy zai sake sakawa ka maida ni” “Wannan yanci ne na har abada, it mean forever...” Ta sake dubansa kamar yadda yake kallonta. “Ina mai baki hakuri akan duk wani abu da na yi miki, wanda kika sani da wanda baki sani ba Yusura, bankwana ne na har abada” Her heart and body star shaking idanuwanta suka tara hawaye. “Na gode da kika taya ni aje farinciki mahaifiyata har sai da ta bar duniya. Yanzu kam kina da yancin ki auri wanda kike so ki yi rayuwar da kike so” Ya juya ya fara tafiya, ta juya tana kallonsa? Me yasa yau ta ji dabam? Ta dade tana jiran zuwan ranar amman ta kasa farinciki, wacam karon ta jidadi da ya sake ta amman ta kasa farinciki. “Yaran fa?” Ya juyo ya kalleta hawaye ya gani suna fitowa daga idonta suna zuba a fuskarta. “Zan kula da su” “Za su fi jindadin zama a gurina” Ya taka zuwa inda take tsaye. “Idan haka kike so, zan minta, but only on one condition, no matter how happen a raye ko a mace zaki fadawa yaran nan cewar mahaifinsu yana kaunarsu, duk wani abun bacin rai ko bakinciki da zai biyo baya ko ya biyo i still love them, ki fada musu mahaifinsu yayi kokari ganin ya tsare duka hakkinsu sai abun da ya fi karfinsu” Ya juya ya nufi kofa sai ta risina kasa ta kira sunansa. “Ka yafe min Kareem, na cutar da kai na sani, kiyayya bata bari na yi biyayya ba” “Komai ya kare yanzu Yusura it over now” Ya amsa mata ba tare fa ya juyo ba ya fice daga falon. Yana shiga motarsa ya murza key mai gadi ya bude masa gate ya dauki hanyar da zata sadashi da gurin aikinsa. Be yi nisa da gida ba hudu ya rufe masa ido kansa ya fara juyawa yana ta kokarin controlling motar amman ya kasa. NOOR POV. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Abun da na fada kenan a lokacin da na farka da karfi, sakamakon mummunan mafarkin da na yi. Wai muna tafiya a jirgi sai ya muka fado kasa ni har da ni ciki, na bugi icce har sai da hankalina ya gushe. Addu'a na yi na neman tsari daga mummunan mafarki. Na yi a'uzubillahi har karshe na tofar dama na sake yi na tofar hagu, sai haki nake kamar wanda ta yi yaki, hannu na kai na lalaba ban ji Abdull ba, sai na sauka daga kan gadon na kunna wuta na nufi bathroom din da nake jin motsin ruwa na tsaya jiran ya fito na shiga. Da na lura ba shi da niyar fitowa sai na tura kofar na fara lekawa babu kowa a ciki, shiga na yi ciki da mamaki, tab din ne a kunne ruwa na zuba kadan kadan amman babu kowa a ciki. Kashewa na yi na bayan na gama fitsari wata kila ya manta ya bar shi a kunne ne. Sai da na nufo gado na zauna sai kuma wata zuciyar ta tambaye ni ina ya tafi? Bargon na sake yayewa na sauko da kafafuwana ina mikewa tsaye sai gashi ya shigo dakin. “Ina ka tafi?” “Ruwan na ji na hada tea, ina zaki ke?” “Ai dai ba zan bata ba a gidana ko? Idan bana dakin nan ina falo ko kitchen” Ya hauro saman gadon ya kwanata rai a bace kamar an masa wani abun, har ya manta be kashe wutar ba, wata kila tambaya ta ce ta bata masa rai. Sauka na yi na kashe wutar na dawo na kwanta. It's not Free pay 500 to Zenith Bank Hadiza Abubakar 2451879008 And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0 KAREEM POV. Dagowa yayi daga rubutun da yake a diary ya kalli Safeena dake zaune gabansa fuska a murtuke kamar an mata mutuwa. “I thought na fada maki bana bukatar sake ganinki?” A take ta yi murmushi. “Ta ina zaka so ganina ka samu sabuwar mace? Ka ba ni mamaki Kareem, ashe zaka iya bude zuciyarka wata ta shiga not just zuciyarka jikinka ma zaka iya hadawa da ita?” “For the very last time ko ki fita ko na saka security su fitar da ke” Wannan karon dariya ta yi. “Ashe zaka iya wulakanta ni saboda wata banzar bazara, me ta fi kwarewa akai? Karamar yarinyar kamar Noor zata dauke maka hankali” “Karki sake zaginta, tana gidan mijinki tana zaman aure noor ba karuwa ba ce, ta san mutumcin aurenta” Ta runtse ido kadan ta tauna halshenta. “Ni da kai ne ba mu san darajar aure ba kenan? Da rarrashi na zo gurin amman na lura gaba daya ta canja maka tunani akaina ta canja maka kwakwalwa, shikenan” Ta mike tsaye. “Daman na zo nan ne na ji, cikin dake jikinta na mijina ne ko naka?” Kareem ya watsa mata wani mugun kallo. “Ita fa ba fasika ba ce” “Kawai dai na tambaya ne, saboda na sani kamar yadda ita ma ta san cewa dan da na haifa yanzu naka ne” Ya kalleta without blinking try to connect his heart with his brain. “You're stupid...” Ta yi murmushi “Yau har na kai haka? Lallai Kareem kai ba dan goyo ba ne, cikin kanen lokaci ka canja min, gaba daya yarinyar nan ta dauke maka hankali, haka mijina yanzu ba shi da lokaci na” “Daman mijinki be taba lokacinki ba, dan haka karki zargi Noor, idan ya koma garin da yake manta ki yake yana can yana sha'aninsa kina na ki” “Muna na mu dai” Ta gyara masa tana kallon idonsa cikin bakin rai. “Me yarinyar nan ta tare miki ne wai? Baki da magana sai na ta” Ta zagayo Inda yake yana ganin hakan ya mike tsaye. “saboda ita ta kwace min kai, a rayuwa kai ne kadai mutumen da zaka nesanta da ni, azabar son ka ta azabtar da ni na kasa hakuri da kai, da ba haka kake ba, amman zuwan yarinyar gaba daya ka sauya min kuma ka kwashe sirrinmu gaba daya ka fada mata, har tana yakata da shi, baka jin kunyar mu'alama da mata har biyu? Bayan karyar da ka yi min akan Yusura?” “Ban taba hada shimfida da Noor ba, kuma ba zan taba ba har abada, indai har sai ta kazantacciyar hanya zan samu Noor, to ina rokon Allah ya hana min ita har abada, kuma aure take a yanzu bana fatan ya mutu, fatana ta samu kwanciyar hankali a ko'ina zata kasancewa?” Ta dan matsa baya. “Baka taba kaiwa jikinta ba? To me ya dauke hankalinka ka fada mata sirrinmu? Ba na mu'alama kadai ba wai har na haihuwar da muka yi?” “What? You're not serious? Taya za fada mata abun da ba ayi ba?” Ta matso kusa da shi tana kallon wayar idonsa. “Miye ba a ayi ba a ciki? Haihuwa ko alaka?” “Na ji na fada mata alaka, amman yaushe muka haihuwa balle na fada mata?” “Yanzu kuma kokarin wasa kake da hankalina?” “Wane irin wasa da hankali? Karya kika mata cewar mun haihu ne? Idan ma kin yi haka to kin yi akan aurenki ne kina kashe kanki ne, domin Noor baki ba linzami ce” Ta kalli gefe sannan ta sake kallonsa. “Taya zan fada mata sirrina? Kai ka fada mata, shiyasa da ta zo gidana ta fada min magana son ranta” Ya fisgota ya rike cinyar hannunta. “Stop talking about Noor, yaushe muk haihu? Are you out of your mind?” Ta fisge hannunta. “Ai na fada maka tun ina da ciki ko? A asibitin nan aka karbi haihuwa danka, kuma Wallahi jininka ne! Au kenan baka yarda ba da na fada maka? Ka dauka karya nake?” Kareem ya daka mata tsawa. “Yaushe rabon da na yi wani abu da ke? Akwai dai abun da kike kokarin yi Safeena” “Babu abun da nake kokarin yi, ni ba zan iya cutar da kai ba, amman ďan da na haifa yanzu Wallahi naka ne, last haduwar da muka yi na samu cikin, sati biyu na kara akan lokacin da nake period a satin Abdull ya dawo, yana barin garin nan naje aka min test aka ce ina da ciki dan sati uku, yaron da na haifa yanzu idan aka kalleshi kallon kurilla za a san cewar danka ne, idan baka yarda zan kawo shi ka gwada jininsa” He lost his temper when he was saying. “Baki da hankali Safeena? Taya zaki aje ciki i mean taya zaki haihu? Dan Haram ne Safeena kuma ki dauka ki kawai mijinki? Ina da aure da yaya safeena kina da aure da yaya taya zaki yi haka?” Ya fadi zaune yana rufe bakinsa. “I don't believe you?” “Na kawo maka yaron ka auna?” Ya kalleta. “Idan gaskiya me ye hujjarki na aikata haka?” Ta risina a gabansa. “So so ne, Kareem ina kaunarka ba zan iya zubarwa ba, ko da ba zan same ka ba zan so aje jininka, kuma waya sani ko nan gaba mu kasance ma'aurata” “Ina zamu kai zunubin Safeena? Ga na zina ga na daukar alhaki? Mu dauki alhakin yaron mu dauki na mijinki? Why how? Why why why Safeena why?” “Ni ma bayan na haihu na yi tunanin be kamata mu yi haka ba, amman komai ai ya riga da ya faru, kuma ba a kanmu farau ba, suna nan da yawa yaran da ba na iyayensu ba” Ya kalleta babu alamar wasa ya ce. “Je ki dauko yaron” Ta mike tsaye ta dauki jakarta ta fice daga office din. Fuskarsa ya shafa yana jin gumi na karyo masa, daman da ta fada masa tana dauke da cikinsa gaskiya ta fada? Ya dauka tana masa wasa ne ko barazana shiyasa ta dawo asibitin. Kuma tun bayan rabuwa da ita be sake bincikarta komai ba saboda yana tunanin ya yanke alaka da ita. Ya mike tsaye yana jin kamar baya iya numfashi. “I can't believe this ba gaskiya ba ne, Kareem” Ya fadawa kansa yana nufar windows din ya rika gaba daya ya rasa me ke masa dadi. Juyowa yayi da karfi ya dauki keys dinsa ya fice daga restaurant din gaba daya. Gurin aikinsa ya koma, ya kira waya ya sanar mata inda yake, a can Safeena ta kai masa yaron mai cike da koshin lafiya mai jiki da haske gwanin sha'awa. Tun da Safeena ta aje yaron yana kallonsa gabansa na faduwa domin ya ga kamaninsa a fuskar yaron, ta dayan gefen kuma yana kama da Safeena. Be ce mata komai ya fita office din, babu jiwa ya dawo sanye da safar hannu ya debi jinin yaron a syringe. “Idan har abun da kika fada ya tabbata Safeena kin cutar da ni, kin cutar da kanki kuma kin cutar da yaron nan” Ta kalli yadda yake kuka bayan Kareem ya dauki jininsa ta ce. “Abu ne da zamu iya ajewa, mijina be sani ba, matarka bata sani ba, to mu bar shi a boye mana, sirrinmu ne ai” Be sake ce mata komai ba ya fice daga office din. Tun tana jiran dawowarsa har ta gaji ta tashi ta fita. Be bar asibitin ba sai da ya debi nashi ya hada ya kai laboratory suka auna masa. He wait they sai da aka hada results aka ba shi. Tsoron abun da zai gani ya saka shi kasa duba takardar har ya shiga motarsa. Ta zauna a motar na tsawon awa daya yana tunanin yadda rayuwa zata kasance masa a yanzu, idan har ta tabbata dansa ne, idan a gurin wasu ba abun kunya ba ne shi a gurinsa abun kunya ne. Daker ya ja motar ya fice daga asibitin, be yi nisa ba ya faka gefe titi ya kai hannu ya dauki result din ya duba. Booom..... Zuciyarsa ta buga da karfi, gaskiya Safeena ta fada, dansa ne jininsa ne. “Why Safeena Why?” Na hade takardar da karfi ya yaga ya jefar ya bugu sitiyarin motar da karfi, ya bude motar ya fita ya fara tafiya sai kuma ya juyo ya dawo ya halbi motar da kafarsa. Ya jingina ya rufe ido ya zai yi? Me yasa ya aikata tun farko? Yaya kenan yanzu? Ya bude motar ya shiga ya kwantar da kujerar motar ya kwanta ya rufe ido. Be daga ba sai da lokacin sallah magariba yayi, a wani masallaci dake kusa da gurin yayi sallah Magariba ya kasa fitowa masallacin har aka yi sallah Isha'i. Sai kusan Tara da rabi ya doshi gidansa. Yana driving yana jin kamar kar ya tafi, kunya hada ido da iyalinsa yake duk kuwa da kasancewar ba su san komai akai ba. Harabar gidan ya faka ya kwanta a motar ba bachi yake ba tunanin yadda zai tafi da wasu abubuwa yake. Yana tuna shawarwarin da abokinsa ya ba shi lokacin da yake raye. Da kuma yadda zuciya ta debi shi ta saka idonsa ya rufe a lokacin ya kasa fahimtar illar da Zina zata yi a rayuwarsa. Ya sani duk wani abu da Allah yace kar a kusance shi, ba abu ne mai kyau ba. Ba ma karku aikata ba kar ma kusanci inda take balle har ku aikata haka Allah ya fada, amman ya take sanin ya murje ido ya aikata, yanzu wa gari ya waya? Kamar zai fadi haka ya bude motar ya fito jikinsa babu kuzari. Sai da ya daga kansa sama ya kalli gidan gabas da yamma sannan ya taka ya isa bakin kofar falon ya shiga. A hankali yake takawa har ya haura sama, dakin yaransa ya fara turawa sai ya samu suna bachi an kashe wutar dakin an kunna musu ocean, sakin kofar yayi ya shiga cikin dakin dakin ya zauna kusa akan gadon Tine yana kallonta kamin ya juya ya kalli Areef. “Maybe nan gaba ku ji kun tsane ni, idan ina raye ko a mace, ku yi bakinciki da na kasance ubanku, kuna da yancin yin haka, domin na bar muku abun kunya, bayan ni kuma nawa iyayen ba su bar min abun kunya ba, sun yi kokarin tsare mutuncinsu da na mu” Ya hade yawu. “Ni dai na san ba zan kashe yaron nan ba, duk wani abun da zan biyo baya dole na karbe shi domin ni na aikata, but no matter what ku sani ina matukar kaunarku kuma ina kokarin na tsare mutuncinku, saboda kar na lalata Future dinku” Ya shafa kan Tine ya sumbance ta, sannan ya tashi ya nufi dayan ma ya shafa kansa ya sumbance shi, ya kallesu cike da bakinciki sannan ya fice daga dakin ya ja musu kofa. Dakinsa ya shiga, yadda ya shigo sanye da talkami da kananan kaya haka ya fada saman gadonsa ya rufe ido, ko agogonsa be iya cirewa ba. Haka ya kwanta har safe ko kadan be yi bachi ba, sai juyi yake idan ya gaji da kwanciyar sai ya sauko kasa ya zauna. Sai da asuba ya siya motsawa ya cire tufafin jikinsa da talkamin ya shiga bandaki yayi wanka tare da alwala ya shimfida carpet, nafila ya fara yi sannan ya gabatar da farilla. A lokacin da ya daga hannunsa zai roki Allah sai kunya ta kama shi, ba zai iya komai ba sai kuka, to me zai ce Allah yayi masa bayan ya bijirewa umarninsa ya bi son zuciyarsa? Allah ya hana shi kuma ya aikata, yanzu kuma ya roki me? Mafita? Ko yafiya? Shafa hannayensa yayi a fuskarsa ya kwanta a gurin feeling so hopeless. Kansa har wani nauyi yayi tsabar damuwa da fargaba da suka same shi lokaci daya, ga kuma rashin bachin da be yi ba gaba daya daren jiya. Usually yaransa suna tafiya makaranta ne ba tare da jiran su ganshi ba, wani lokacin ko da za su tafi yana bachi, Yusura kuma ta koya musu idan yana bachi basa tashinsa. But yau sai ya sha banban da sauran ranakun, Areef ya fara shigowa rike da jakar abincinsa Tine na bayansa, Kareem na jin motsinsu sai ya rufe idonsa not like he don't want to see their faces but kunyar kallonsu yake kuma bakinciki zai taso masa ne. “Bachi yake Areef mu tafi” Areef be ji maganar yayarsa ba sai da ya leka fuskar mahaifinsa ya ga da gaske bachin yake sannan ya juya suka yafi. Suna fita Kareem ya bude idonsa yana kallon ceiling da raunannin idanuwansa. Ya tashi zaune, ya dafe kansa, gaba daya ganin yake kamar ranar jiya ba gaskiya bace mafarki ne. Misalin tara ya shirya cikin kananan kayan babu zancen saka agogo ko shafa mai turare da ya zame masa dole kawai ya tsaya domin baya iya rayuwa babu kamshi. Gefen gadonsa ya zauna ya bude drawersa ya dauko diary da pen yayi rubutu a kai ya nade ya aje pen din ya mike tsaye ya dauki wayarsa ya fice daga dakin. Da dai daya ya rika taka stairs din yana saukowa yana kallon Yusura dake goge dinning kanta babu dankwali. Damuwa ta bayyana karara a fuskarsa kyawawan idanuwansa sun fada sun yi ja sosai irin na wanda be ga bachi ba bachi be ganshi ba. Kusa da ita ya karasa ya aje mata takardar a dinning. For the first time ever ta ji gabanta ya fadi irin faduwar da be taba ba. Ta kalli takardar ta kalleshi. “Miye a ciki?” Ya kalleta. “Yancinki ne, yancin da kika dade kina nema” Ta hade abu da karfi. “Babu amfani Daddy zai sake sakawa ka maida ni” “Wannan yanci ne na har abada, it mean forever...” Ta sake dubansa kamar yadda yake kallonta. “Ina mai baki hakuri akan duk wani abu da na yi miki, wanda kika sani da wanda baki sani ba Yusura, bankwana ne na har abada” Her heart and body star shaking idanuwanta suka tara hawaye. “Na gode da kika taya ni aje farinciki mahaifiyata har sai da ta bar duniya. Yanzu kam kina da yancin ki auri wanda kike so ki yi rayuwar da kike so” Ya juya ya fara tafiya, ta juya tana kallonsa? Me yasa yau ta ji dabam? Ta dade tana jiran zuwan ranar amman ta kasa farinciki, wacam karon ta jidadi da ya sake ta amman ta kasa farinciki. “Yaran fa?” Ya juyo ya kalleta hawaye ya gani suna fitowa daga idonta suna zuba a fuskarta. “Zan kula da su” “Za su fi jindadin zama a gurina” Ya taka zuwa inda take tsaye. “Idan haka kike so, zan minta, but only on one condition, no matter how happen a raye ko a mace zaki fadawa yaran nan cewar mahaifinsu yana kaunarsu, duk wani abun bacin rai ko bakinciki da zai biyo baya ko ya biyo i still love them, ki fada musu mahaifinsu yayi kokari ganin ya tsare duka hakkinsu sai abun da ya fi karfinsu” Ya juya ya nufi kofa sai ta risina kasa ta kira sunansa. “Ka yafe min Kareem, na cutar da kai na sani, kiyayya bata bari na yi biyayya ba” “Komai ya kare yanzu Yusura it over now” Ya amsa mata ba tare fa ya juyo ba ya fice daga falon. Yana shiga motarsa ya murza key mai gadi ya bude masa gate ya dauki hanyar da zata sadashi da gurin aikinsa. Be yi nisa da gida ba hudu ya rufe masa ido kansa ya fara juyawa yana ta kokarin controlling motar amman ya kasa. NOOR POV. “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Abun da na fada kenan a lokacin da na farka da karfi, sakamakon mummunan mafarkin da na yi. Wai muna tafiya a jirgi sai ya muka fado kasa ni har da ni ciki, na bugi icce har sai da hankalina ya gushe. Addu'a na yi na neman tsari daga mummunan mafarki. Na yi a'uzubillahi har karshe na tofar dama na sake yi na tofar hagu, sai haki nake kamar wanda ta yi yaki, hannu na kai na lalaba ban ji Abdull ba, sai na sauka daga kan gadon na kunna wuta na nufi bathroom din da nake jin motsin ruwa na tsaya jiran ya fito na shiga. Da na lura ba shi da niyar fitowa sai na tura kofar na fara lekawa babu kowa a ciki, shiga na yi ciki da mamaki, tab din ne a kunne ruwa na zuba kadan kadan amman babu kowa a ciki. Kashewa na yi na bayan na gama fitsari wata kila ya manta ya bar shi a kunne ne. Sai da na nufo gado na zauna sai kuma wata zuciyar ta tambaye ni ina ya tafi? Bargon na sake yayewa na sauko da kafafuwana ina mikewa tsaye sai gashi ya shigo dakin. “Ina ka tafi?” “Ruwan na ji na hada tea, ina zaki ke?” “Ai dai ba zan bata ba a gidana ko? Idan bana dakin nan ina falo ko kitchen” Ya hauro saman gadon ya kwanata rai a bace kamar an masa wani abun, har ya manta be kashe wutar ba, wata kila tambaya ta ce ta bata masa rai. Sauka na yi na kashe wutar na dawo na kwanta. It's not Free pay 500 to Zenith Bank Hadiza Abubakar 2451879008 And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0 Washe Gari na tashi da wuri saboda zan tafi asibiti, dan haka na gyara da wuri na fito falo, ina jin motsin Hana na nufi kitchen din na dan rikawa mata aiki. Ina tsaka da kashe socket ta yi min wata magana da ta saka na kalleta. “Noor ina son na tafi gida” “Me yasa Baba ya sake magana ne?” “Aa kawai dai ina son gida yanzu, na fi jindadin zama gida sama da nan” Na juyo da kyau na fuskance. “Hana wani abu na yi miki ba daidai ba ko Abdull yayi miki?” “Aa ba ko daya, kawai dai na fi sha'awar tafiya gida ne” Na dan jimm ina mamakin dalilinta na fadar haka a yanzu, daman na lura yanayinta gaba daya ya canja. “Hana mafarki kika yi marar kyau ko me?” “Ba komai ni dai kawai ina son na tafi gida” “To kije ki dawo ko kuma ki koma gidan gaba daya?” “Gaba daya dai nake son na koma” “Karatunkin fa?” “Zan hakura na san idan naje can Mama zata iya sakani idan Baba ya yarda” Na matsa kusa da ita domin babu ta yadda lafiya zata saka ya yanke karatunta ta koma gida haka nan kawai sai da dalili. “Hana na san muma yawan samun tsabani da ke a gida, amman nan gidan aurena ne, idan kina ganin akwai abun da nake miki da baya miki dadi zaki iya fada min sai na gyara, idan kuma aiki ne kike ganin na sakar miki ragamarsa zan rika yin rabi, amman dan Allah ki zauna ina jindadin zamanki ina son yar'uwa a kusa da ni, ba ni da kowa nan zamanki a gidan nan yana rage min kewa” “Babu wani tsabani da zamu samu har ya saka na ji bana bukarki a kusa da ni, mu na samu tsabani a gida a nan ma zamu iya samu, saboda zama tare dole wata rana zaka ji an maka ba daidai ba, amman Noor ni ba zan iya cin amanarki ba” Ta rumgume ni tana kuka, jikina yayi sanyi sosai kalaminta na karshe ya saka min shakku a zuciya. “Akwai abun da yake faruwa tsakaninki da Abdull ne?” Ta dago da sauri. “Aa Wallahi Babu, dan Allah karki zarge shi ki lalata aurenki, Wallahi Wallahi na rantse miki da Allah babu wani abu tsakanina da Abdull” Hankali ya dan kwanta da ta yi min rantsuwa cewar ba tsakaninta da Abdull ba ne. “To ya kawo zancen cin amana Hana?” Ta share hawayenta. “Ina nufin kamar na guje ki saboda kin min wani laifi, ai kamar na ci amanarki ne a matsayinki na yar'uwata” “To me yasa kike son tafiya gida? Kina karatunki a nan, Abdull ma idan ya ji ai zai yi fada, Mama ma sai ta miki fada tace kin san ba zaki karatu ba kika saka bata kudi aka biya miki har na shekara uku” “Kawai ina yawan mafarkin marar kyau ne, kuma ana baki tsoro a gidan nan ina tunanin akwai aljannu a gidan” “To ki rika addu'a mana Hana, ke da kike fada min yadda zan bi da rayuwa na jidadi yau kuma ke kika rasa ya zaki yi?” Ta yi murmushi “Gaba daya na rikice mugun mafarkin da na yi ya daga min hankali” Zan sake yin magana Abdull ya kirani. “Noor kin fasa zuwa awon ne? Karki makara fa” Na dauki ruwan zafi na fice daga kitchen, sai da ta jera mana komai a dinning sannan ta zuba nata ta dauka. “Lafiya na ga kamar yanayinta ya canja” Abdull ya tambaya she dai shi ma ya lura da yadda take ta hade rai bata son kallon kowa. “Lafiya kalau” Ta wuce dakinta bayan ta amsa mishi, da kallo na bita sai da ta shige sannan na juyo na kalleshi, kamar na fada masa kudurinta sai kuma wata zuciyar ta hana ni, na san ba abu ne da zai masa dadi ba, saboda kudin makaranta da ya biya mata ga yawan hidima da yake mata, tafiya makaranta ma kullum sai ya bata kudin bus kuma ya rage mata hanya saboda akwai tazara daga unguwarmu zuwa makaranta kuma babu abun hawa sosai ta gurarenmu sai idan sun kawo Passenger. “Ina jin bata da lafiya ne” “Me yake damunta? Ko kuma dai mood swings ne” “Yeah” Ko da muka gama karyawa ta yi shirin makaranta da uniform dinta da suke sakawa kullum. Tare muka fita sai da ya fara sauketa sannan ya sauke ni a asibitin ya wuce gurin aikinsa. Tun daga ranar Hana bata sake yi min maganar komawa gida ba, sai dai na lura da yanayinta gaba daya ya canja kamar zaman gidan ya daina mata dadi a yanzu, domin ko hirar da take zama muna yi tare da Abdull a da yanzu duk ta daina, ko da yake yanzu ba kamar da ba ne, da take gida kullum yanzu kuma idan ta tafi bata dawowa sai yamma idan ta dawo wani sa'in ta hau aikin gida ko da ta gama kuma sai bachi. Sai can ba a rasa ba muke zama muna hira a falo da zarar Abdull ya shigo zata masa sannu da zuwa ta shige dakinta ba zata sake fitowa sai gobe. Ko wani abun ya siyo sai dai na kai mata nata dakinta, ko kuma shi ya kwankwasa kofar dakin ya aje mata daga bakin kofa, wani sa'in idan ina jin wahalar tashi. Wata kila ta fara haduwa da abokan banza masu hore mata kunne ne, ko kuma dai ta gaji da yin aikin gida ne, ko kuma nata gidan mijin take son tafiya ita ma. Ko ma dai yaya ne na daure ma zuciyata na zauna da ita a haka, saboda bana son ta lakata karatunta a lokacin da take tsananin bukatarsa, kuma ana yi da kai ya fi ba'ayi, zamanta yana taimaka min ko yaya ne tun da ita take min komai a gidan kuma ina ganinta na san ina da yar'uwa a kusa ina jin sanyi a haka din ma. KAREEM POV. Da sauri ya maida idon ya rufe ya kai hannunsa dake sanye da drip ya murza idon sannan ya sake budewa. Hannun ya kai ya cire robar dake bakinsa yana kokarin daga hannunsa daya sai ya ji yayi masa nauyi dubawar da zai yi sai yayi arba kan dansa Areef a hannun. Yunkurawa yayi a haka ya tashi zaune ya saka dayan hannun a hankali ya cire hannunsa. Haka ya cire duk wani abu da aka laka masa sannan ya sauko da kafafuwansa yana tuna abun da ya faru. Ya san dai yana tsaka da tuki hudu ya sauko masa daga lokacin kuma be sake sanin inda yake ba, maybe ya hadari yayi, ba ma wata kila idan be yi hadarin ba ai ba za a kawo shi nan a aje ba. But why ICU shi da be ji ciwo ko daya a jikinsa ba, domin be ga wani guri da ya ji ciwo bako ya bugu. Hannu ya mika ya janyo files dinsa ya bude ya duba. Daman ya sani zama unconscious or in a critical condition ke saka a aje mutum a gurin. Ya duba ya gani kwanansa biyu a dakin amman be sani ba sai yau da ya farka, babu wata rauni a jikinsa but hankalinsa da numfashi sun yi nisan da an dauka barin duniyar zai yi. Ko me ua buga oho, ya san dai hakan baya rasa nasara da damuwar da yake ciki, kusan ita ce silar faruwa komai. Ya aje files din ya shafa kan dansa dake sanye da uniform din makaranta yana murmushi ko dan yaran nan yana bukatar rayuwa. Areef ya bude ido sakamakon shafa kansa da Dadynsa yayi. “Hey young Man” Yaron ya tashi zaune ya matsa ya rumgume mahaifinsa yana murna. “Dady ka farka” Kareem ya saka hannu ya shafa bayansa yana murmushi kamin wani azababben ciwo ya ratsa zuciyarsa har sai da ya ji ta motsa kamar ta bar muhallinta. “Oh...” Ya furta Areef ya dago ya kalleshi. “Dady minene?” Kareem ya murmushi. “Ba komai ina Tine” “Suna waje bari na kira ta har da Mama ma tana nan, kullum zai mun zo kana bachi, Hajiya tana nan ita da Uncle Aaryan nan yake kwana” Har ya isa kofa sai kuma ya juyo ya kalleshi. “Daddy ma kullum yana zuwa, yana yin addu'a yana tofa maka, Dady kuma Momy ta kwashe kayanta gaba daya ta koma gurin Hajiya an bata bangare daya tace tare zata zauna da mu” Kareem ya daga mishi kai. Areef ya fita da gudunsa, Kareem kuma ya mike tsaye ya fito daga dakin da kafafuwa normal yake jin kansa kamar be yi hadari ba. Ya san yadda asibitin take fa kuma dokokinta sai ya canja ma kansa daki bayan ya gaisa da ma'aikatan dake ta masa sannu Doctor dake duty yana da tsokarsa yana fadin ya bari yayi aikinsa yanzu shi majinyaci ne ba likita ba Files din dake dayan dakin likita ya dauko ya dawo da su sabon dakin da Kareem yake, sannan aka bawa visitors damar shiga, yan'uwa na ta shigowa suna masa sannu na nesa kuma suna kira a waya. Duk wani motsi nasa yana kan idon Yusura kallonsa take sosai kamar bata taba ganinsa ba, sau daya ta yi masa ya jiki bata sake ba sai dai duk dagowar da zai yi sai ya ga tana kallonsa. Tun daga ranar kuma bata sake zuwa ba duba shi har aka sallame shi after four day's da yayi a asibitin. Ranar da zai bar asibitin babu yadda Hajiya bata yi ba akan ya dawo family house ya zauna har sai jikin ya kara warwarewa da kyau saboda a can gidan babu kowa a yanzu amman ya ki, domin baya son zama gidan zai fi sakewa a gida ko da kuwa ba shi da lafiyar balle baya jin ciwon komai a jikinsa. Taya zai saki matarsa ta tare a family house dinsu shi ma ya koma can ya tare kamar mace. Ba karamin godiya yayi ma Allah ba lokacin da Aaryam ya kai shi gidan ya ga yadda gaban motarsa ya lalace, bayan ma ya bugu ba karamin accident yayi ba amman Allah ya kawo masa sauki tun da be ji rauni a ko'ina ba. Aaryam ya fada masa yadda hadarin ya afko sai da ya cika da tsananin mamaki. “Babu wanda ya dauka zaka rayu fa, Wallahi duk mun tsorata, babba mota ka buga irin mai zube yashin tefa. Mai motar yace yana ta maka horn domin ya ga yadda ka zo da gudu amman baka tsaya ba sai da ka bugu shi, gashi ita kuma wata motar ta bugi taka a baya, daker aka fito da kai motar babu rauni amman baka numfashi hankali ya bace gaba daya, asibitin ma sai da aka yi da gaske sannan numfashinka ya dawo” Yayi murmushi. “Kwana ne ba su kare ba, da lokacin yayi da ba zan farka ba, Alhamdullahi” “Gaskiya mun auna arziki, da mun rasa ka rayuwa ba zata yi dadi ba” Kareem ya kalli falon ya mike tsaye. “Wata rana dole za ku rasa ni Aaryan dole kuma ayi hakuri da rayuwar” “Haka ne, amman ba ma fatan zuwanta yanzu, Allah dai ya kara maka lafiya” “Ameen” Aayam ya sauke ajiyar zuciya. “Yusura da Khadija sun sha kuka, Hajiya har sai da aka zuba mata ruwa, ban taba ganinta cikin tashin hankali irin na ranar ba, babu wanda be yi kuka ba sai ni” Kareem ya juyo ya kalleshi. “Eh kai mai zuciyar fir'auna ko?” Aaryam yayi dariya. “Ai duk abun da zai saka namiji kuka ba karamin abu ba ne, Allah dai ya tsare faruwar hakan” Dinning Kareem ya dafa. “Yusura bata fada muku abun da ya faru ba?” “Ta fada mana, har ta kwashe kayanta ai Hajiya ta bata bangare daya ta zauna saboda ta samu sakewa ita da yaranta, Khadija da Nana sun koma bangarenta, na yi mamakin kukanta wata kila ita ma ta dauka mutuwa zaka yi” “Daddy be ce komai ba a game da rabuwarmu?” “Ba ka da matsala da shi, tun a lokacin da aka fada min halin da kake ciki sai na same shi na yi masa bayanin komai, saboda mu samu goyon bayansa idan zaka kara aure, ashe Allah da kai ba, amman dai ya sani kuma ya daga maka kafa. Kawai addu'a yayi Allah yasa hakan shi ne mafi alheri” Dogon numfashi Kareem yaja ya sauke ya daga kansa sama. “Ameen” A gidan Aaryam ya wuni saboda ya ragewa dan'uwansa Zango har sai da yamma ta yi sannan ya tafi bayan sun sha hira sosai. Kareem ya juyo kenan daga rakiyar da yayi ma Aaryan bakin kofar falon sako ya shigo wayarsa. “Wata kila ni ce silar hadarinka? Shin ka aikata hakan ne da nufin kashe kanka? Ka ji zafin gaskiyar da ka sani ne Kareem? Ni ma daga baya na gane ban kyauta ba na yi kuskure, amman na maka alkwari babu wanda zai ji wannan, ina zuwa dubaka asibiti a kullum amman bana samun damar shiga na ganka saboda yan'uwanka da matarka suna gurin. Yau kuma na tafi aka ce an sallame ka na jidadin haka kuma na ji tausayinka na yi bakinciki abun da ua faru da kai, ina kaunarka Kareem Wallahi ina kaunarka” Ya goge sakon bayan ya gama karantawa, ko ya fada mata yayi hadarin ma oho, falon ya shiga ya kwanta akan kujera ya rufe ido yana maida numfashi a hankali. NOOR POV. A lokacin da cikina ya shiga wata bakwai na samu sauki abubuwa da yawa na daina amai da kwadayin sosai, ko zabar abinci. Har ta kai ni nake shirya abun karyawa da safe da kaina. Domin yanzu Hana ce mai tsananin bachin safe idan ta gama sallah ta koma ta kwana sai kace ba yar makaranta ba. Kullum sai ta buga latti saboda bachi, har tausayi take ba ni domin na san wahala ce ta yi mata yawa, na aikin gida da take ga kuma karatu da basa daga kafa. Abun sai ya zame mana kamar duty ni ce mai saurin bachin dare ita kuma ta yi rankon na safe. Domin da zarar na gama sallah Isha'i Abdull ya kawo lemun juice da yake hada min a kullum, domin likita yace na rika cin yayan itatuwa sosai a yanzu fiye da kayan zafi ko kwadayi irin su madara da danginsu. Saboda kina yana ta girma ne a yanzu, ban yi kasa a guiwa ba na rumgumi kayan marmari, kullum sai na ci da dare kuma sai Abdull ya hada min lemun juice da juicer da ya siya gurin Khadeeja Candy Store, zallar ruwan fruit take matsewa sai dan sukari kadan da yake kasa min ko kuma abar da bana so wato zuma, wani lokacin saboda bakin nawa ya saba da zaki idan babu ba zan sha ba. Da zarar ya hada min na sha sai bachi yayi gaba da ni, ko motsi ba zan yi ba sai safe. Ina tsaka da shafa face cream ya shigo dakin ya aje min cup din natural orange juice. Sannan ya nufi wardrobe ya bude ya dauko kayan bachinsa ya saka. “Kina bukatar wani abu?” Na kalleshi kamar na ce ina da bukatar ka, yau wata shida kenan ban hada shimfida da mijina ba, tun cikina na wata daya da yan kwanaki ya nade sha'awata ya jefar saboda kawai na ki yarda a zubar da cikin. Sai kuma wata zuciyar tace na daure mana na zuba masa ido tun da haka ya zaba. “Aa” “Okay to zaki yi kallo?” “Aa bachi zan yi” “Yanzu ai kin lalace da bachin dare, da dare yayi sai bachi kamin tara na dare ta yi har kin kai Morocco, Allah yasa ba raguwa ko rago zaki haifa ba, wannan lalaci yayi yawa” Na yi dariya mai sauti ina masa gwalo. “Bachin yana min dadi, da na kwanta bana sanin me duniya take ciki sai na farka” “Asha bachi lafiya Mom Unborn” Ya fice ya bar ni na cigaba da shafa face cream din, sai da na gama sannan na dauki lemun juice din na sha kadan sai na ji zakin zumar yayi min yawa gashi ba son zuma nake sosai ba, haka na saka dole na tashi na shiga bathroom na kunna tap na tara lemun na kara ruwa kadan, na kashe juyowar da zan yi santsin tile ya kwashe ni, aiko ba shiri na saki kofin na rike tab din sai kofin ya fadi kasa lemun ya zube. “Allah ya tsare na auna arziki yau kai...” Na fada ina hakki, da na fadi gurin ba karamin ciwo zan ji ba, waya sani ma ko na karye tun da jikin babu karfi. Ruwa na saka na wanke lemun da ya zube na dauke kofin da ya tsaga na fito na aje shi a inda na saba ajewa na hau gadon na yi addu'a na kwanta, nan da nan kuwa bachi yace wa yake jira ba ni ba, kamar na mutu haka na fara bachin ban san shigowar Abdull dakin ba, kashe wuta da yayi ma duk ban sani ba. Daman bana sanin komai sai safe. Ina tunanin shan lemun yana taimaka min sosai gurin samun bachi mai dadi kuma mai nauyi da tsayi, domin yau da ban shanye shi gaba daya ba na farka sai dai ban kai ga motsawa ba na ji saukar Abdull daga kan gadon ya nufi bathroom, yana shiga na ji kararar ruwa be jima ba ya fito ina kallonsa ya rufe kofar a hankali ba tare da ya kashe ruwan ba. Mamaki ya cika kwakwalwata ashe har yanzu be daina wannan abun ba, domin tun a wacan lokacin zuciyata take raya min yana biyawa kansa bukata ne a bandakin. Ina ganin ya dauki wayarsa sai na rufe idona, na yi zaton bandakin zai koma sai gashi ya kunna fitilar wayar ya haska fuskata. Ni kuma na yi kamar bachin nake da gaske har sai da ya kauce sannan na bude ido. Ga mamaki na sai na ga ya nufi kofar fita ya bude a hankali ya fice. Zumut na tashi zaune kamar ledar da iska ya dauka. Na zauna gurin da tsawon minti biyar ban ji ya dawo ba, sai na sauko daga kan gadon na bude bandakin na kunna guluf na duba sannan na kashe na janyo kofar na rufe a yadda take. Takawa na yi na fita dakin, a tunanin yana falo ne, sai dai kuma ban same shi a falon ba, domin wutar falon ma a kashe take ban ga hasken wayarsa ba kuma ban ga alamar mutum ba ta dan hasken waje da yake shigowa. Na nufi ma kunnun wutar kamar zan kunna sai kuma na fasa na nufi kitchen na leka nan ma baya nan. Na juyowa na nufo dakina da mamaki domin ko kadan zuciyata ba ta raya min abun da kunnuwa za su ji ba. Daf da zan shiga dakina ne na ji karar rufe kofar dakin Hana wata kila kuma na bandakinta ne yayi kara har na ji saboda dare ne, hakan ya saka hankalina ya karkata can, to daman idan baya falo baya kitchen baya dakina ina zai je? Waje? A tsakar daren nan ba zai fita waje ba sai idan da wani babban dalili. Na taka cikin faduwar gaba na doshi kofar dakin, na kai hannu zan murda da nufin na bude na shiga sai kuma dauke hannuna na matsa kusa na dora kunne na a kofar dakin. Shiruuuu ban ji wani motsi ba, na sauke ajiyar zuciya ina jin kamar hankali ya kwanta, ashe dan'uwansa ne ke tafe da gumurzunsa irin tafiyar da ban yi tsammani ba. “Sai yaushe za a zubar to?” Na ji muryarta, hakan ya sakan ni kwantar da kunne a jikin kofar sosai na natsu numfashi ma daker nake fitarwa saboda na ji me take fada. “Kina da matsala ne ke Wallahi, na fada miki ni ai na san lokacin da ya kamata a zubar ko?” “Tsoro nake kar ya girma, kuma ina tsoron na sha wahala” Ta fada cikin muryar kuka. “Ai na sani idan ban ja lokaci haka ba, ba zan samu hadin kanki ba, yanzu ana zubarwa kuma ba zaki sake yarda da ni ba” Rarararararsssssssaaaa. Gabana ya bugawar da mai sauraren tsawa dake tafe da ruwa. “Zan yarda, ni dai dan Allah a zubar” “Kin yi alkawari?” “Eh, dan Allah a zubar” “Ki kwantar da hankalinki mana, na san abun da zan yi, kin san ina sonki sosai ai, ina son ki Hana, amman ki yi ta wahalar da ni, Wallahi da ace ke na fara gani ba zan auri yayarki ba...” Ban sake jin komai ba sai shesshekar kukanta kadan kadan. Tashin hankali ne be bari na sake jin komai ba ko kuma dai ba su sake cewa ba din. Na dauke kunne na shafa wuyana ina lalaben sarkar da babu ita a wuyana. Jikina ya fara rawa hawaye suka yi ambaliya a idona. Na shiga na same su a ciki na nuna musu na sa komai, ko dai wai ban ji daidai ba, ko dai gizo kunnuwa suke min. Na bar kofar na fara takawa na nufi dakina na shiga na hau gadona na kwanta na rufe ido na tsawon min biyu sannan na bude. Wai ko zan ji cewar mafarki, amman ban ga alamar haka ba. Na mari kaina sai na ji zafin na tsara kunci na, tabbas gaske ne ba mafarki nake ba. Amman taya? Kanwata ce fa uwa daya uba daya, kanwata da mijina? Kanwata ta jini mai bina, kanwata da muka kwanta a mahaifa daya ciki daya uwa daya ta kawo mu duniya? Kuma mijina mijin da nake aure auren sunna! Mijin da nake dauke da cikin dansa ko diyarsa. Tun yaushe haka take faruwa? Na mike tsaye na nufi madubi na sai kuma na zauna a kasa. Me na yi da na cancanci haka? Why me? Why? Kanwata? Jinina? “Wayyo Allah na” Na dafa zuciyata sai wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya ya zo min. Wannan abun yayi min muni ina ji a wasu gurare amman ban dauka abun zai zo kusa ni ba. Na tashi daker na koma saman gadon na kwanta jikina na rawa na takure guri daya na rumgume fillo, a wannan daren bachi be samu damar ziyarta idona ba, kunci be bar ni, kamin safe zazzabi ya rufe ni, filon da na rumgume kuma ya jike da hawaye na. Abdull be dawo dakin ba sai asuba, ina jin shigowarsa da lokacin da ya kwanta saman gadon ya lulluba... Littafin nan ba kyauta ba ne. Biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to Zenith Bank Hadiza Abubakar 2451879008 And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0 Washe Gari na tashi da wuri saboda zan tafi asibiti, dan haka na gyara da wuri na fito falo, ina jin motsin Hana na nufi kitchen din na dan rikawa mata aiki. Ina tsaka da kashe socket ta yi min wata magana da ta saka na kalleta. “Noor ina son na tafi gida” “Me yasa Baba ya sake magana ne?” “Aa kawai dai ina son gida yanzu, na fi jindadin zama gida sama da nan” Na juyo da kyau na fuskance. “Hana wani abu na yi miki ba daidai ba ko Abdull yayi miki?” “Aa ba ko daya, kawai dai na fi sha'awar tafiya gida ne” Na dan jimm ina mamakin dalilinta na fadar haka a yanzu, daman na lura yanayinta gaba daya ya canja. “Hana mafarki kika yi marar kyau ko me?” “Ba komai ni dai kawai ina son na tafi gida” “To kije ki dawo ko kuma ki koma gidan gaba daya?” “Gaba daya dai nake son na koma” “Karatunkin fa?” “Zan hakura na san idan naje can Mama zata iya sakani idan Baba ya yarda” Na matsa kusa da ita domin babu ta yadda lafiya zata saka ya yanke karatunta ta koma gida haka nan kawai sai da dalili. “Hana na san muma yawan samun tsabani da ke a gida, amman nan gidan aurena ne, idan kina ganin akwai abun da nake miki da baya miki dadi zaki iya fada min sai na gyara, idan kuma aiki ne kike ganin na sakar miki ragamarsa zan rika yin rabi, amman dan Allah ki zauna ina jindadin zamanki ina son yar'uwa a kusa da ni, ba ni da kowa nan zamanki a gidan nan yana rage min kewa” “Babu wani tsabani da zamu samu har ya saka na ji bana bukarki a kusa da ni, mu na samu tsabani a gida a nan ma zamu iya samu, saboda zama tare dole wata rana zaka ji an maka ba daidai ba, amman Noor ni ba zan iya cin amanarki ba” Ta rumgume ni tana kuka, jikina yayi sanyi sosai kalaminta na karshe ya saka min shakku a zuciya. “Akwai abun da yake faruwa tsakaninki da Abdull ne?” Ta dago da sauri. “Aa Wallahi Babu, dan Allah karki zarge shi ki lalata aurenki, Wallahi Wallahi na rantse miki da Allah babu wani abu tsakanina da Abdull” Hankali ya dan kwanta da ta yi min rantsuwa cewar ba tsakaninta da Abdull ba ne. “To ya kawo zancen cin amana Hana?” Ta share hawayenta. “Ina nufin kamar na guje ki saboda kin min wani laifi, ai kamar na ci amanarki ne a matsayinki na yar'uwata” “To me yasa kike son tafiya gida? Kina karatunki a nan, Abdull ma idan ya ji ai zai yi fada, Mama ma sai ta miki fada tace kin san ba zaki karatu ba kika saka bata kudi aka biya miki har na shekara uku” “Kawai ina yawan mafarkin marar kyau ne, kuma ana baki tsoro a gidan nan ina tunanin akwai aljannu a gidan” “To ki rika addu'a mana Hana, ke da kike fada min yadda zan bi da rayuwa na jidadi yau kuma ke kika rasa ya zaki yi?” Ta yi murmushi “Gaba daya na rikice mugun mafarkin da na yi ya daga min hankali” Zan sake yin magana Abdull ya kirani. “Noor kin fasa zuwa awon ne? Karki makara fa” Na dauki ruwan zafi na fice daga kitchen, sai da ta jera mana komai a dinning sannan ta zuba nata ta dauka. “Lafiya na ga kamar yanayinta ya canja” Abdull ya tambaya she dai shi ma ya lura da yadda take ta hade rai bata son kallon kowa. “Lafiya kalau” Ta wuce dakinta bayan ta amsa mishi, da kallo na bita sai da ta shige sannan na juyo na kalleshi, kamar na fada masa kudurinta sai kuma wata zuciyar ta hana ni, na san ba abu ne da zai masa dadi ba, saboda kudin makaranta da ya biya mata ga yawan hidima da yake mata, tafiya makaranta ma kullum sai ya bata kudin bus kuma ya rage mata hanya saboda akwai tazara daga unguwarmu zuwa makaranta kuma babu abun hawa sosai ta gurarenmu sai idan sun kawo Passenger. “Ina jin bata da lafiya ne” “Me yake damunta? Ko kuma dai mood swings ne” “Yeah” Ko da muka gama karyawa ta yi shirin makaranta da uniform dinta da suke sakawa kullum. Tare muka fita sai da ya fara sauketa sannan ya sauke ni a asibitin ya wuce gurin aikinsa. Tun daga ranar Hana bata sake yi min maganar komawa gida ba, sai dai na lura da yanayinta gaba daya ya canja kamar zaman gidan ya daina mata dadi a yanzu, domin ko hirar da take zama muna yi tare da Abdull a da yanzu duk ta daina, ko da yake yanzu ba kamar da ba ne, da take gida kullum yanzu kuma idan ta tafi bata dawowa sai yamma idan ta dawo wani sa'in ta hau aikin gida ko da ta gama kuma sai bachi. Sai can ba a rasa ba muke zama muna hira a falo da zarar Abdull ya shigo zata masa sannu da zuwa ta shige dakinta ba zata sake fitowa sai gobe. Ko wani abun ya siyo sai dai na kai mata nata dakinta, ko kuma shi ya kwankwasa kofar dakin ya aje mata daga bakin kofa, wani sa'in idan ina jin wahalar tashi. Wata kila ta fara haduwa da abokan banza masu hore mata kunne ne, ko kuma dai ta gaji da yin aikin gida ne, ko kuma nata gidan mijin take son tafiya ita ma. Ko ma dai yaya ne na daure ma zuciyata na zauna da ita a haka, saboda bana son ta lakata karatunta a lokacin da take tsananin bukatarsa, kuma ana yi da kai ya fi ba'ayi, zamanta yana taimaka min ko yaya ne tun da ita take min komai a gidan kuma ina ganinta na san ina da yar'uwa a kusa ina jin sanyi a haka din ma. KAREEM POV. Da sauri ya maida idon ya rufe ya kai hannunsa dake sanye da drip ya murza idon sannan ya sake budewa. Hannun ya kai ya cire robar dake bakinsa yana kokarin daga hannunsa daya sai ya ji yayi masa nauyi dubawar da zai yi sai yayi arba kan dansa Areef a hannun. Yunkurawa yayi a haka ya tashi zaune ya saka dayan hannun a hankali ya cire hannunsa. Haka ya cire duk wani abu da aka laka masa sannan ya sauko da kafafuwansa yana tuna abun da ya faru. Ya san dai yana tsaka da tuki hudu ya sauko masa daga lokacin kuma be sake sanin inda yake ba, maybe ya hadari yayi, ba ma wata kila idan be yi hadarin ba ai ba za a kawo shi nan a aje ba. But why ICU shi da be ji ciwo ko daya a jikinsa ba, domin be ga wani guri da ya ji ciwo bako ya bugu. Hannu ya mika ya janyo files dinsa ya bude ya duba. Daman ya sani zama unconscious or in a critical condition ke saka a aje mutum a gurin. Ya duba ya gani kwanansa biyu a dakin amman be sani ba sai yau da ya farka, babu wata rauni a jikinsa but hankalinsa da numfashi sun yi nisan da an dauka barin duniyar zai yi. Ko me ua buga oho, ya san dai hakan baya rasa nasara da damuwar da yake ciki, kusan ita ce silar faruwa komai. Ya aje files din ya shafa kan dansa dake sanye da uniform din makaranta yana murmushi ko dan yaran nan yana bukatar rayuwa. Areef ya bude ido sakamakon shafa kansa da Dadynsa yayi. “Hey young Man” Yaron ya tashi zaune ya matsa ya rumgume mahaifinsa yana murna. “Dady ka farka” Kareem ya saka hannu ya shafa bayansa yana murmushi kamin wani azababben ciwo ya ratsa zuciyarsa har sai da ya ji ta motsa kamar ta bar muhallinta. “Oh...” Ya furta Areef ya dago ya kalleshi. “Dady minene?” Kareem ya murmushi. “Ba komai ina Tine” “Suna waje bari na kira ta har da Mama ma tana nan, kullum zai mun zo kana bachi, Hajiya tana nan ita da Uncle Aaryan nan yake kwana” Har ya isa kofa sai kuma ya juyo ya kalleshi. “Daddy ma kullum yana zuwa, yana yin addu'a yana tofa maka, Dady kuma Momy ta kwashe kayanta gaba daya ta koma gurin Hajiya an bata bangare daya tace tare zata zauna da mu” Kareem ya daga mishi kai. Areef ya fita da gudunsa, Kareem kuma ya mike tsaye ya fito daga dakin da kafafuwa normal yake jin kansa kamar be yi hadari ba. Ya san yadda asibitin take fa kuma dokokinta sai ya canja ma kansa daki bayan ya gaisa da ma'aikatan dake ta masa sannu Doctor dake duty yana da tsokarsa yana fadin ya bari yayi aikinsa yanzu shi majinyaci ne ba likita ba Files din dake dayan dakin likita ya dauko ya dawo da su sabon dakin da Kareem yake, sannan aka bawa visitors damar shiga, yan'uwa na ta shigowa suna masa sannu na nesa kuma suna kira a waya. Duk wani motsi nasa yana kan idon Yusura kallonsa take sosai kamar bata taba ganinsa ba, sau daya ta yi masa ya jiki bata sake ba sai dai duk dagowar da zai yi sai ya ga tana kallonsa. Tun daga ranar kuma bata sake zuwa ba duba shi har aka sallame shi after four day's da yayi a asibitin. Ranar da zai bar asibitin babu yadda Hajiya bata yi ba akan ya dawo family house ya zauna har sai jikin ya kara warwarewa da kyau saboda a can gidan babu kowa a yanzu amman ya ki, domin baya son zama gidan zai fi sakewa a gida ko da kuwa ba shi da lafiyar balle baya jin ciwon komai a jikinsa. Taya zai saki matarsa ta tare a family house dinsu shi ma ya koma can ya tare kamar mace. Ba karamin godiya yayi ma Allah ba lokacin da Aaryam ya kai shi gidan ya ga yadda gaban motarsa ya lalace, bayan ma ya bugu ba karamin accident yayi ba amman Allah ya kawo masa sauki tun da be ji rauni a ko'ina ba. Aaryam ya fada masa yadda hadarin ya afko sai da ya cika da tsananin mamaki. “Babu wanda ya dauka zaka rayu fa, Wallahi duk mun tsorata, babba mota ka buga irin mai zube yashin tefa. Mai motar yace yana ta maka horn domin ya ga yadda ka zo da gudu amman baka tsaya ba sai da ka bugu shi, gashi ita kuma wata motar ta bugi taka a baya, daker aka fito da kai motar babu rauni amman baka numfashi hankali ya bace gaba daya, asibitin ma sai da aka yi da gaske sannan numfashinka ya dawo” Yayi murmushi. “Kwana ne ba su kare ba, da lokacin yayi da ba zan farka ba, Alhamdullahi” “Gaskiya mun auna arziki, da mun rasa ka rayuwa ba zata yi dadi ba” Kareem ya kalli falon ya mike tsaye. “Wata rana dole za ku rasa ni Aaryan dole kuma ayi hakuri da rayuwar” “Haka ne, amman ba ma fatan zuwanta yanzu, Allah dai ya kara maka lafiya” “Ameen” Aayam ya sauke ajiyar zuciya. “Yusura da Khadija sun sha kuka, Hajiya har sai da aka zuba mata ruwa, ban taba ganinta cikin tashin hankali irin na ranar ba, babu wanda be yi kuka ba sai ni” Kareem ya juyo ya kalleshi. “Eh kai mai zuciyar fir'auna ko?” Aaryam yayi dariya. “Ai duk abun da zai saka namiji kuka ba karamin abu ba ne, Allah dai ya tsare faruwar hakan” Dinning Kareem ya dafa. “Yusura bata fada muku abun da ya faru ba?” “Ta fada mana, har ta kwashe kayanta ai Hajiya ta bata bangare daya ta zauna saboda ta samu sakewa ita da yaranta, Khadija da Nana sun koma bangarenta, na yi mamakin kukanta wata kila ita ma ta dauka mutuwa zaka yi” “Daddy be ce komai ba a game da rabuwarmu?” “Ba ka da matsala da shi, tun a lokacin da aka fada min halin da kake ciki sai na same shi na yi masa bayanin komai, saboda mu samu goyon bayansa idan zaka kara aure, ashe Allah da kai ba, amman dai ya sani kuma ya daga maka kafa. Kawai addu'a yayi Allah yasa hakan shi ne mafi alheri” Dogon numfashi Kareem yaja ya sauke ya daga kansa sama. “Ameen” A gidan Aaryam ya wuni saboda ya ragewa dan'uwansa Zango har sai da yamma ta yi sannan ya tafi bayan sun sha hira sosai. Kareem ya juyo kenan daga rakiyar da yayi ma Aaryan bakin kofar falon sako ya shigo wayarsa. “Wata kila ni ce silar hadarinka? Shin ka aikata hakan ne da nufin kashe kanka? Ka ji zafin gaskiyar da ka sani ne Kareem? Ni ma daga baya na gane ban kyauta ba na yi kuskure, amman na maka alkwari babu wanda zai ji wannan, ina zuwa dubaka asibiti a kullum amman bana samun damar shiga na ganka saboda yan'uwanka da matarka suna gurin. Yau kuma na tafi aka ce an sallame ka na jidadin haka kuma na ji tausayinka na yi bakinciki abun da ua faru da kai, ina kaunarka Kareem Wallahi ina kaunarka” Ya goge sakon bayan ya gama karantawa, ko ya fada mata yayi hadarin ma oho, falon ya shiga ya kwanta akan kujera ya rufe ido yana maida numfashi a hankali. NOOR POV. A lokacin da cikina ya shiga wata bakwai na samu sauki abubuwa da yawa na daina amai da kwadayin sosai, ko zabar abinci. Har ta kai ni nake shirya abun karyawa da safe da kaina. Domin yanzu Hana ce mai tsananin bachin safe idan ta gama sallah ta koma ta kwana sai kace ba yar makaranta ba. Kullum sai ta buga latti saboda bachi, har tausayi take ba ni domin na san wahala ce ta yi mata yawa, na aikin gida da take ga kuma karatu da basa daga kafa. Abun sai ya zame mana kamar duty ni ce mai saurin bachin dare ita kuma ta yi rankon na safe. Domin da zarar na gama sallah Isha'i Abdull ya kawo lemun juice da yake hada min a kullum, domin likita yace na rika cin yayan itatuwa sosai a yanzu fiye da kayan zafi ko kwadayi irin su madara da danginsu. Saboda kina yana ta girma ne a yanzu, ban yi kasa a guiwa ba na rumgumi kayan marmari, kullum sai na ci da dare kuma sai Abdull ya hada min lemun juice da juicer da ya siya gurin Khadeeja Candy Store, zallar ruwan fruit take matsewa sai dan sukari kadan da yake kasa min ko kuma abar da bana so wato zuma, wani lokacin saboda bakin nawa ya saba da zaki idan babu ba zan sha ba. Da zarar ya hada min na sha sai bachi yayi gaba da ni, ko motsi ba zan yi ba sai safe. Ina tsaka da shafa face cream ya shigo dakin ya aje min cup din natural orange juice. Sannan ya nufi wardrobe ya bude ya dauko kayan bachinsa ya saka. “Kina bukatar wani abu?” Na kalleshi kamar na ce ina da bukatar ka, yau wata shida kenan ban hada shimfida da mijina ba, tun cikina na wata daya da yan kwanaki ya nade sha'awata ya jefar saboda kawai na ki yarda a zubar da cikin. Sai kuma wata zuciyar tace na daure mana na zuba masa ido tun da haka ya zaba. “Aa” “Okay to zaki yi kallo?” “Aa bachi zan yi” “Yanzu ai kin lalace da bachin dare, da dare yayi sai bachi kamin tara na dare ta yi har kin kai Morocco, Allah yasa ba raguwa ko rago zaki haifa ba, wannan lalaci yayi yawa” Na yi dariya mai sauti ina masa gwalo. “Bachin yana min dadi, da na kwanta bana sanin me duniya take ciki sai na farka” “Asha bachi lafiya Mom Unborn” Ya fice ya bar ni na cigaba da shafa face cream din, sai da na gama sannan na dauki lemun juice din na sha kadan sai na ji zakin zumar yayi min yawa gashi ba son zuma nake sosai ba, haka na saka dole na tashi na shiga bathroom na kunna tap na tara lemun na kara ruwa kadan, na kashe juyowar da zan yi santsin tile ya kwashe ni, aiko ba shiri na saki kofin na rike tab din sai kofin ya fadi kasa lemun ya zube. “Allah ya tsare na auna arziki yau kai...” Na fada ina hakki, da na fadi gurin ba karamin ciwo zan ji ba, waya sani ma ko na karye tun da jikin babu karfi. Ruwa na saka na wanke lemun da ya zube na dauke kofin da ya tsaga na fito na aje shi a inda na saba ajewa na hau gadon na yi addu'a na kwanta, nan da nan kuwa bachi yace wa yake jira ba ni ba, kamar na mutu haka na fara bachin ban san shigowar Abdull dakin ba, kashe wuta da yayi ma duk ban sani ba. Daman bana sanin komai sai safe. Ina tunanin shan lemun yana taimaka min sosai gurin samun bachi mai dadi kuma mai nauyi da tsayi, domin yau da ban shanye shi gaba daya ba na farka sai dai ban kai ga motsawa ba na ji saukar Abdull daga kan gadon ya nufi bathroom, yana shiga na ji kararar ruwa be jima ba ya fito ina kallonsa ya rufe kofar a hankali ba tare da ya kashe ruwan ba. Mamaki ya cika kwakwalwata ashe har yanzu be daina wannan abun ba, domin tun a wacan lokacin zuciyata take raya min yana biyawa kansa bukata ne a bandakin. Ina ganin ya dauki wayarsa sai na rufe idona, na yi zaton bandakin zai koma sai gashi ya kunna fitilar wayar ya haska fuskata. Ni kuma na yi kamar bachin nake da gaske har sai da ya kauce sannan na bude ido. Ga mamaki na sai na ga ya nufi kofar fita ya bude a hankali ya fice. Zumut na tashi zaune kamar ledar da iska ya dauka. Na zauna gurin da tsawon minti biyar ban ji ya dawo ba, sai na sauko daga kan gadon na bude bandakin na kunna guluf na duba sannan na kashe na janyo kofar na rufe a yadda take. Takawa na yi na fita dakin, a tunanin yana falo ne, sai dai kuma ban same shi a falon ba, domin wutar falon ma a kashe take ban ga hasken wayarsa ba kuma ban ga alamar mutum ba ta dan hasken waje da yake shigowa. Na nufi ma kunnun wutar kamar zan kunna sai kuma na fasa na nufi kitchen na leka nan ma baya nan. Na juyowa na nufo dakina da mamaki domin ko kadan zuciyata ba ta raya min abun da kunnuwa za su ji ba. Daf da zan shiga dakina ne na ji karar rufe kofar dakin Hana wata kila kuma na bandakinta ne yayi kara har na ji saboda dare ne, hakan ya saka hankalina ya karkata can, to daman idan baya falo baya kitchen baya dakina ina zai je? Waje? A tsakar daren nan ba zai fita waje ba sai idan da wani babban dalili. Na taka cikin faduwar gaba na doshi kofar dakin, na kai hannu zan murda da nufin na bude na shiga sai kuma dauke hannuna na matsa kusa na dora kunne na a kofar dakin. Shiruuuu ban ji wani motsi ba, na sauke ajiyar zuciya ina jin kamar hankali ya kwanta, ashe dan'uwansa ne ke tafe da gumurzunsa irin tafiyar da ban yi tsammani ba. “Sai yaushe za a zubar to?” Na ji muryarta, hakan ya sakan ni kwantar da kunne a jikin kofar sosai na natsu numfashi ma daker nake fitarwa saboda na ji me take fada. “Kina da matsala ne ke Wallahi, na fada miki ni ai na san lokacin da ya kamata a zubar ko?” “Tsoro nake kar ya girma, kuma ina tsoron na sha wahala” Ta fada cikin muryar kuka. “Ai na sani idan ban ja lokaci haka ba, ba zan samu hadin kanki ba, yanzu ana zubarwa kuma ba zaki sake yarda da ni ba” Rarararararsssssssaaaa. Gabana ya bugawar da mai sauraren tsawa dake tafe da ruwa. “Zan yarda, ni dai dan Allah a zubar” “Kin yi alkawari?” “Eh, dan Allah a zubar” “Ki kwantar da hankalinki mana, na san abun da zan yi, kin san ina sonki sosai ai, ina son ki Hana, amman ki yi ta wahalar da ni, Wallahi da ace ke na fara gani ba zan auri yayarki ba...” Ban sake jin komai ba sai shesshekar kukanta kadan kadan. Tashin hankali ne be bari na sake jin komai ba ko kuma dai ba su sake cewa ba din. Na dauke kunne na shafa wuyana ina lalaben sarkar da babu ita a wuyana. Jikina ya fara rawa hawaye suka yi ambaliya a idona. Na shiga na same su a ciki na nuna musu na sa komai, ko dai wai ban ji daidai ba, ko dai gizo kunnuwa suke min. Na bar kofar na fara takawa na nufi dakina na shiga na hau gadona na kwanta na rufe ido na tsawon min biyu sannan na bude. Wai ko zan ji cewar mafarki, amman ban ga alamar haka ba. Na mari kaina sai na ji zafin na tsara kunci na, tabbas gaske ne ba mafarki nake ba. Amman taya? Kanwata ce fa uwa daya uba daya, kanwata da mijina? Kanwata ta jini mai bina, kanwata da muka kwanta a mahaifa daya ciki daya uwa daya ta kawo mu duniya? Kuma mijina mijin da nake aure auren sunna! Mijin da nake dauke da cikin dansa ko diyarsa. Tun yaushe haka take faruwa? Na mike tsaye na nufi madubi na sai kuma na zauna a kasa. Me na yi da na cancanci haka? Why me? Why? Kanwata? Jinina? “Wayyo Allah na” Na dafa zuciyata sai wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya ya zo min. Wannan abun yayi min muni ina ji a wasu gurare amman ban dauka abun zai zo kusa ni ba. Na tashi daker na koma saman gadon na kwanta jikina na rawa na takure guri daya na rumgume fillo, a wannan daren bachi be samu damar ziyarta idona ba, kunci be bar ni, kamin safe zazzabi ya rufe ni, filon da na rumgume kuma ya jike da hawaye na. Abdull be dawo dakin ba sai asuba, ina jin shigowarsa da lokacin da ya kwanta saman gadon ya lulluba... Littafin nan ba kyauta ba ne. Biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to Zenith Bank Hadiza Abubakar 2451879008 And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0 Washe Gari na tashi da wuri saboda zan tafi asibiti, dan haka na gyara da wuri na fito falo, ina jin motsin Hana na nufi kitchen din na dan rikawa mata aiki. Ina tsaka da kashe socket ta yi min wata magana da ta saka na kalleta. “Noor ina son na tafi gida” “Me yasa Baba ya sake magana ne?” “Aa kawai dai ina son gida yanzu, na fi jindadin zama gida sama da nan” Na juyo da kyau na fuskance. “Hana wani abu na yi miki ba daidai ba ko Abdull yayi miki?” “Aa ba ko daya, kawai dai na fi sha'awar tafiya gida ne” Na dan jimm ina mamakin dalilinta na fadar haka a yanzu, daman na lura yanayinta gaba daya ya canja. “Hana mafarki kika yi marar kyau ko me?” “Ba komai ni dai kawai ina son na tafi gida” “To kije ki dawo ko kuma ki koma gidan gaba daya?” “Gaba daya dai nake son na koma” “Karatunkin fa?” “Zan hakura na san idan naje can Mama zata iya sakani idan Baba ya yarda” Na matsa kusa da ita domin babu ta yadda lafiya zata saka ya yanke karatunta ta koma gida haka nan kawai sai da dalili. “Hana na san muma yawan samun tsabani da ke a gida, amman nan gidan aurena ne, idan kina ganin akwai abun da nake miki da baya miki dadi zaki iya fada min sai na gyara, idan kuma aiki ne kike ganin na sakar miki ragamarsa zan rika yin rabi, amman dan Allah ki zauna ina jindadin zamanki ina son yar'uwa a kusa da ni, ba ni da kowa nan zamanki a gidan nan yana rage min kewa” “Babu wani tsabani da zamu samu har ya saka na ji bana bukarki a kusa da ni, mu na samu tsabani a gida a nan ma zamu iya samu, saboda zama tare dole wata rana zaka ji an maka ba daidai ba, amman Noor ni ba zan iya cin amanarki ba” Ta rumgume ni tana kuka, jikina yayi sanyi sosai kalaminta na karshe ya saka min shakku a zuciya. “Akwai abun da yake faruwa tsakaninki da Abdull ne?” Ta dago da sauri. “Aa Wallahi Babu, dan Allah karki zarge shi ki lalata aurenki, Wallahi Wallahi na rantse miki da Allah babu wani abu tsakanina da Abdull” Hankali ya dan kwanta da ta yi min rantsuwa cewar ba tsakaninta da Abdull ba ne. “To ya kawo zancen cin amana Hana?” Ta share hawayenta. “Ina nufin kamar na guje ki saboda kin min wani laifi, ai kamar na ci amanarki ne a matsayinki na yar'uwata” “To me yasa kike son tafiya gida? Kina karatunki a nan, Abdull ma idan ya ji ai zai yi fada, Mama ma sai ta miki fada tace kin san ba zaki karatu ba kika saka bata kudi aka biya miki har na shekara uku” “Kawai ina yawan mafarkin marar kyau ne, kuma ana baki tsoro a gidan nan ina tunanin akwai aljannu a gidan” “To ki rika addu'a mana Hana, ke da kike fada min yadda zan bi da rayuwa na jidadi yau kuma ke kika rasa ya zaki yi?” Ta yi murmushi “Gaba daya na rikice mugun mafarkin da na yi ya daga min hankali” Zan sake yin magana Abdull ya kirani. “Noor kin fasa zuwa awon ne? Karki makara fa” Na dauki ruwan zafi na fice daga kitchen, sai da ta jera mana komai a dinning sannan ta zuba nata ta dauka. “Lafiya na ga kamar yanayinta ya canja” Abdull ya tambaya she dai shi ma ya lura da yadda take ta hade rai bata son kallon kowa. “Lafiya kalau” Ta wuce dakinta bayan ta amsa mishi, da kallo na bita sai da ta shige sannan na juyo na kalleshi, kamar na fada masa kudurinta sai kuma wata zuciyar ta hana ni, na san ba abu ne da zai masa dadi ba, saboda kudin makaranta da ya biya mata ga yawan hidima da yake mata, tafiya makaranta ma kullum sai ya bata kudin bus kuma ya rage mata hanya saboda akwai tazara daga unguwarmu zuwa makaranta kuma babu abun hawa sosai ta gurarenmu sai idan sun kawo Passenger. “Ina jin bata da lafiya ne” “Me yake damunta? Ko kuma dai mood swings ne” “Yeah” Ko da muka gama karyawa ta yi shirin makaranta da uniform dinta da suke sakawa kullum. Tare muka fita sai da ya fara sauketa sannan ya sauke ni a asibitin ya wuce gurin aikinsa. Tun daga ranar Hana bata sake yi min maganar komawa gida ba, sai dai na lura da yanayinta gaba daya ya canja kamar zaman gidan ya daina mata dadi a yanzu, domin ko hirar da take zama muna yi tare da Abdull a da yanzu duk ta daina, ko da yake yanzu ba kamar da ba ne, da take gida kullum yanzu kuma idan ta tafi bata dawowa sai yamma idan ta dawo wani sa'in ta hau aikin gida ko da ta gama kuma sai bachi. Sai can ba a rasa ba muke zama muna hira a falo da zarar Abdull ya shigo zata masa sannu da zuwa ta shige dakinta ba zata sake fitowa sai gobe. Ko wani abun ya siyo sai dai na kai mata nata dakinta, ko kuma shi ya kwankwasa kofar dakin ya aje mata daga bakin kofa, wani sa'in idan ina jin wahalar tashi. Wata kila ta fara haduwa da abokan banza masu hore mata kunne ne, ko kuma dai ta gaji da yin aikin gida ne, ko kuma nata gidan mijin take son tafiya ita ma. Ko ma dai yaya ne na daure ma zuciyata na zauna da ita a haka, saboda bana son ta lakata karatunta a lokacin da take tsananin bukatarsa, kuma ana yi da kai ya fi ba'ayi, zamanta yana taimaka min ko yaya ne tun da ita take min komai a gidan kuma ina ganinta na san ina da yar'uwa a kusa ina jin sanyi a haka din ma. KAREEM POV. Da sauri ya maida idon ya rufe ya kai hannunsa dake sanye da drip ya murza idon sannan ya sake budewa. Hannun ya kai ya cire robar dake bakinsa yana kokarin daga hannunsa daya sai ya ji yayi masa nauyi dubawar da zai yi sai yayi arba kan dansa Areef a hannun. Yunkurawa yayi a haka ya tashi zaune ya saka dayan hannun a hankali ya cire hannunsa. Haka ya cire duk wani abu da aka laka masa sannan ya sauko da kafafuwansa yana tuna abun da ya faru. Ya san dai yana tsaka da tuki hudu ya sauko masa daga lokacin kuma be sake sanin inda yake ba, maybe ya hadari yayi, ba ma wata kila idan be yi hadarin ba ai ba za a kawo shi nan a aje ba. But why ICU shi da be ji ciwo ko daya a jikinsa ba, domin be ga wani guri da ya ji ciwo bako ya bugu. Hannu ya mika ya janyo files dinsa ya bude ya duba. Daman ya sani zama unconscious or in a critical condition ke saka a aje mutum a gurin. Ya duba ya gani kwanansa biyu a dakin amman be sani ba sai yau da ya farka, babu wata rauni a jikinsa but hankalinsa da numfashi sun yi nisan da an dauka barin duniyar zai yi. Ko me ua buga oho, ya san dai hakan baya rasa nasara da damuwar da yake ciki, kusan ita ce silar faruwa komai. Ya aje files din ya shafa kan dansa dake sanye da uniform din makaranta yana murmushi ko dan yaran nan yana bukatar rayuwa. Areef ya bude ido sakamakon shafa kansa da Dadynsa yayi. “Hey young Man” Yaron ya tashi zaune ya matsa ya rumgume mahaifinsa yana murna. “Dady ka farka” Kareem ya saka hannu ya shafa bayansa yana murmushi kamin wani azababben ciwo ya ratsa zuciyarsa har sai da ya ji ta motsa kamar ta bar muhallinta. “Oh...” Ya furta Areef ya dago ya kalleshi. “Dady minene?” Kareem ya murmushi. “Ba komai ina Tine” “Suna waje bari na kira ta har da Mama ma tana nan, kullum zai mun zo kana bachi, Hajiya tana nan ita da Uncle Aaryan nan yake kwana” Har ya isa kofa sai kuma ya juyo ya kalleshi. “Daddy ma kullum yana zuwa, yana yin addu'a yana tofa maka, Dady kuma Momy ta kwashe kayanta gaba daya ta koma gurin Hajiya an bata bangare daya tace tare zata zauna da mu” Kareem ya daga mishi kai. Areef ya fita da gudunsa, Kareem kuma ya mike tsaye ya fito daga dakin da kafafuwa normal yake jin kansa kamar be yi hadari ba. Ya san yadda asibitin take fa kuma dokokinta sai ya canja ma kansa daki bayan ya gaisa da ma'aikatan dake ta masa sannu Doctor dake duty yana da tsokarsa yana fadin ya bari yayi aikinsa yanzu shi majinyaci ne ba likita ba Files din dake dayan dakin likita ya dauko ya dawo da su sabon dakin da Kareem yake, sannan aka bawa visitors damar shiga, yan'uwa na ta shigowa suna masa sannu na nesa kuma suna kira a waya. Duk wani motsi nasa yana kan idon Yusura kallonsa take sosai kamar bata taba ganinsa ba, sau daya ta yi masa ya jiki bata sake ba sai dai duk dagowar da zai yi sai ya ga tana kallonsa. Tun daga ranar kuma bata sake zuwa ba duba shi har aka sallame shi after four day's da yayi a asibitin. Ranar da zai bar asibitin babu yadda Hajiya bata yi ba akan ya dawo family house ya zauna har sai jikin ya kara warwarewa da kyau saboda a can gidan babu kowa a yanzu amman ya ki, domin baya son zama gidan zai fi sakewa a gida ko da kuwa ba shi da lafiyar balle baya jin ciwon komai a jikinsa. Taya zai saki matarsa ta tare a family house dinsu shi ma ya koma can ya tare kamar mace. Ba karamin godiya yayi ma Allah ba lokacin da Aaryam ya kai shi gidan ya ga yadda gaban motarsa ya lalace, bayan ma ya bugu ba karamin accident yayi ba amman Allah ya kawo masa sauki tun da be ji rauni a ko'ina ba. Aaryam ya fada masa yadda hadarin ya afko sai da ya cika da tsananin mamaki. “Babu wanda ya dauka zaka rayu fa, Wallahi duk mun tsorata, babba mota ka buga irin mai zube yashin tefa. Mai motar yace yana ta maka horn domin ya ga yadda ka zo da gudu amman baka tsaya ba sai da ka bugu shi, gashi ita kuma wata motar ta bugi taka a baya, daker aka fito da kai motar babu rauni amman baka numfashi hankali ya bace gaba daya, asibitin ma sai da aka yi da gaske sannan numfashinka ya dawo” Yayi murmushi. “Kwana ne ba su kare ba, da lokacin yayi da ba zan farka ba, Alhamdullahi” “Gaskiya mun auna arziki, da mun rasa ka rayuwa ba zata yi dadi ba” Kareem ya kalli falon ya mike tsaye. “Wata rana dole za ku rasa ni Aaryan dole kuma ayi hakuri da rayuwar” “Haka ne, amman ba ma fatan zuwanta yanzu, Allah dai ya kara maka lafiya” “Ameen” Aayam ya sauke ajiyar zuciya. “Yusura da Khadija sun sha kuka, Hajiya har sai da aka zuba mata ruwa, ban taba ganinta cikin tashin hankali irin na ranar ba, babu wanda be yi kuka ba sai ni” Kareem ya juyo ya kalleshi. “Eh kai mai zuciyar fir'auna ko?” Aaryam yayi dariya. “Ai duk abun da zai saka namiji kuka ba karamin abu ba ne, Allah dai ya tsare faruwar hakan” Dinning Kareem ya dafa. “Yusura bata fada muku abun da ya faru ba?” “Ta fada mana, har ta kwashe kayanta ai Hajiya ta bata bangare daya ta zauna saboda ta samu sakewa ita da yaranta, Khadija da Nana sun koma bangarenta, na yi mamakin kukanta wata kila ita ma ta dauka mutuwa zaka yi” “Daddy be ce komai ba a game da rabuwarmu?” “Ba ka da matsala da shi, tun a lokacin da aka fada min halin da kake ciki sai na same shi na yi masa bayanin komai, saboda mu samu goyon bayansa idan zaka kara aure, ashe Allah da kai ba, amman dai ya sani kuma ya daga maka kafa. Kawai addu'a yayi Allah yasa hakan shi ne mafi alheri” Dogon numfashi Kareem yaja ya sauke ya daga kansa sama. “Ameen” A gidan Aaryam ya wuni saboda ya ragewa dan'uwansa Zango har sai da yamma ta yi sannan ya tafi bayan sun sha hira sosai. Kareem ya juyo kenan daga rakiyar da yayi ma Aaryan bakin kofar falon sako ya shigo wayarsa. “Wata kila ni ce silar hadarinka? Shin ka aikata hakan ne da nufin kashe kanka? Ka ji zafin gaskiyar da ka sani ne Kareem? Ni ma daga baya na gane ban kyauta ba na yi kuskure, amman na maka alkwari babu wanda zai ji wannan, ina zuwa dubaka asibiti a kullum amman bana samun damar shiga na ganka saboda yan'uwanka da matarka suna gurin. Yau kuma na tafi aka ce an sallame ka na jidadin haka kuma na ji tausayinka na yi bakinciki abun da ua faru da kai, ina kaunarka Kareem Wallahi ina kaunarka” Ya goge sakon bayan ya gama karantawa, ko ya fada mata yayi hadarin ma oho, falon ya shiga ya kwanta akan kujera ya rufe ido yana maida numfashi a hankali. NOOR POV. A lokacin da cikina ya shiga wata bakwai na samu sauki abubuwa da yawa na daina amai da kwadayin sosai, ko zabar abinci. Har ta kai ni nake shirya abun karyawa da safe da kaina. Domin yanzu Hana ce mai tsananin bachin safe idan ta gama sallah ta koma ta kwana sai kace ba yar makaranta ba. Kullum sai ta buga latti saboda bachi, har tausayi take ba ni domin na san wahala ce ta yi mata yawa, na aikin gida da take ga kuma karatu da basa daga kafa. Abun sai ya zame mana kamar duty ni ce mai saurin bachin dare ita kuma ta yi rankon na safe. Domin da zarar na gama sallah Isha'i Abdull ya kawo lemun juice da yake hada min a kullum, domin likita yace na rika cin yayan itatuwa sosai a yanzu fiye da kayan zafi ko kwadayi irin su madara da danginsu. Saboda kina yana ta girma ne a yanzu, ban yi kasa a guiwa ba na rumgumi kayan marmari, kullum sai na ci da dare kuma sai Abdull ya hada min lemun juice da juicer da ya siya gurin Khadeeja Candy Store, zallar ruwan fruit take matsewa sai dan sukari kadan da yake kasa min ko kuma abar da bana so wato zuma, wani lokacin saboda bakin nawa ya saba da zaki idan babu ba zan sha ba. Da zarar ya hada min na sha sai bachi yayi gaba da ni, ko motsi ba zan yi ba sai safe. Ina tsaka da shafa face cream ya shigo dakin ya aje min cup din natural orange juice. Sannan ya nufi wardrobe ya bude ya dauko kayan bachinsa ya saka. “Kina bukatar wani abu?” Na kalleshi kamar na ce ina da bukatar ka, yau wata shida kenan ban hada shimfida da mijina ba, tun cikina na wata daya da yan kwanaki ya nade sha'awata ya jefar saboda kawai na ki yarda a zubar da cikin. Sai kuma wata zuciyar tace na daure mana na zuba masa ido tun da haka ya zaba. “Aa” “Okay to zaki yi kallo?” “Aa bachi zan yi” “Yanzu ai kin lalace da bachin dare, da dare yayi sai bachi kamin tara na dare ta yi har kin kai Morocco, Allah yasa ba raguwa ko rago zaki haifa ba, wannan lalaci yayi yawa” Na yi dariya mai sauti ina masa gwalo. “Bachin yana min dadi, da na kwanta bana sanin me duniya take ciki sai na farka” “Asha bachi lafiya Mom Unborn” Ya fice ya bar ni na cigaba da shafa face cream din, sai da na gama sannan na dauki lemun juice din na sha kadan sai na ji zakin zumar yayi min yawa gashi ba son zuma nake sosai ba, haka na saka dole na tashi na shiga bathroom na kunna tap na tara lemun na kara ruwa kadan, na kashe juyowar da zan yi santsin tile ya kwashe ni, aiko ba shiri na saki kofin na rike tab din sai kofin ya fadi kasa lemun ya zube. “Allah ya tsare na auna arziki yau kai...” Na fada ina hakki, da na fadi gurin ba karamin ciwo zan ji ba, waya sani ma ko na karye tun da jikin babu karfi. Ruwa na saka na wanke lemun da ya zube na dauke kofin da ya tsaga na fito na aje shi a inda na saba ajewa na hau gadon na yi addu'a na kwanta, nan da nan kuwa bachi yace wa yake jira ba ni ba, kamar na mutu haka na fara bachin ban san shigowar Abdull dakin ba, kashe wuta da yayi ma duk ban sani ba. Daman bana sanin komai sai safe. Ina tunanin shan lemun yana taimaka min sosai gurin samun bachi mai dadi kuma mai nauyi da tsayi, domin yau da ban shanye shi gaba daya ba na farka sai dai ban kai ga motsawa ba na ji saukar Abdull daga kan gadon ya nufi bathroom, yana shiga na ji kararar ruwa be jima ba ya fito ina kallonsa ya rufe kofar a hankali ba tare da ya kashe ruwan ba. Mamaki ya cika kwakwalwata ashe har yanzu be daina wannan abun ba, domin tun a wacan lokacin zuciyata take raya min yana biyawa kansa bukata ne a bandakin. Ina ganin ya dauki wayarsa sai na rufe idona, na yi zaton bandakin zai koma sai gashi ya kunna fitilar wayar ya haska fuskata. Ni kuma na yi kamar bachin nake da gaske har sai da ya kauce sannan na bude ido. Ga mamaki na sai na ga ya nufi kofar fita ya bude a hankali ya fice. Zumut na tashi zaune kamar ledar da iska ya dauka. Na zauna gurin da tsawon minti biyar ban ji ya dawo ba, sai na sauko daga kan gadon na bude bandakin na kunna guluf na duba sannan na kashe na janyo kofar na rufe a yadda take. Takawa na yi na fita dakin, a tunanin yana falo ne, sai dai kuma ban same shi a falon ba, domin wutar falon ma a kashe take ban ga hasken wayarsa ba kuma ban ga alamar mutum ba ta dan hasken waje da yake shigowa. Na nufi ma kunnun wutar kamar zan kunna sai kuma na fasa na nufi kitchen na leka nan ma baya nan. Na juyowa na nufo dakina da mamaki domin ko kadan zuciyata ba ta raya min abun da kunnuwa za su ji ba. Daf da zan shiga dakina ne na ji karar rufe kofar dakin Hana wata kila kuma na bandakinta ne yayi kara har na ji saboda dare ne, hakan ya saka hankalina ya karkata can, to daman idan baya falo baya kitchen baya dakina ina zai je? Waje? A tsakar daren nan ba zai fita waje ba sai idan da wani babban dalili. Na taka cikin faduwar gaba na doshi kofar dakin, na kai hannu zan murda da nufin na bude na shiga sai kuma dauke hannuna na matsa kusa na dora kunne na a kofar dakin. Shiruuuu ban ji wani motsi ba, na sauke ajiyar zuciya ina jin kamar hankali ya kwanta, ashe dan'uwansa ne ke tafe da gumurzunsa irin tafiyar da ban yi tsammani ba. “Sai yaushe za a zubar to?” Na ji muryarta, hakan ya sakan ni kwantar da kunne a jikin kofar sosai na natsu numfashi ma daker nake fitarwa saboda na ji me take fada. “Kina da matsala ne ke Wallahi, na fada miki ni ai na san lokacin da ya kamata a zubar ko?” “Tsoro nake kar ya girma, kuma ina tsoron na sha wahala” Ta fada cikin muryar kuka. “Ai na sani idan ban ja lokaci haka ba, ba zan samu hadin kanki ba, yanzu ana zubarwa kuma ba zaki sake yarda da ni ba” Rarararararsssssssaaaa. Gabana ya bugawar da mai sauraren tsawa dake tafe da ruwa. “Zan yarda, ni dai dan Allah a zubar” “Kin yi alkawari?” “Eh, dan Allah a zubar” “Ki kwantar da hankalinki mana, na san abun da zan yi, kin san ina sonki sosai ai, ina son ki Hana, amman ki yi ta wahalar da ni, Wallahi da ace ke na fara gani ba zan auri yayarki ba...” Ban sake jin komai ba sai shesshekar kukanta kadan kadan. Tashin hankali ne be bari na sake jin komai ba ko kuma dai ba su sake cewa ba din. Na dauke kunne na shafa wuyana ina lalaben sarkar da babu ita a wuyana. Jikina ya fara rawa hawaye suka yi ambaliya a idona. Na shiga na same su a ciki na nuna musu na sa komai, ko dai wai ban ji daidai ba, ko dai gizo kunnuwa suke min. Na bar kofar na fara takawa na nufi dakina na shiga na hau gadona na kwanta na rufe ido na tsawon min biyu sannan na bude. Wai ko zan ji cewar mafarki, amman ban ga alamar haka ba. Na mari kaina sai na ji zafin na tsara kunci na, tabbas gaske ne ba mafarki nake ba. Amman taya? Kanwata ce fa uwa daya uba daya, kanwata da mijina? Kanwata ta jini mai bina, kanwata da muka kwanta a mahaifa daya ciki daya uwa daya ta kawo mu duniya? Kuma mijina mijin da nake aure auren sunna! Mijin da nake dauke da cikin dansa ko diyarsa. Tun yaushe haka take faruwa? Na mike tsaye na nufi madubi na sai kuma na zauna a kasa. Me na yi da na cancanci haka? Why me? Why? Kanwata? Jinina? “Wayyo Allah na” Na dafa zuciyata sai wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya ya zo min. Wannan abun yayi min muni ina ji a wasu gurare amman ban dauka abun zai zo kusa ni ba. Na tashi daker na koma saman gadon na kwanta jikina na rawa na takure guri daya na rumgume fillo, a wannan daren bachi be samu damar ziyarta idona ba, kunci be bar ni, kamin safe zazzabi ya rufe ni, filon da na rumgume kuma ya jike da hawaye na. Abdull be dawo dakin ba sai asuba, ina jin shigowarsa da lokacin da ya kwanta saman gadon ya lulluba... Littafin nan ba kyauta ba ne. Biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to Zenith Bank Hadiza Abubakar 2451879008 And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.Be dade da kwanciya ba na ji nishanrinsa alamar bachi mai nauyi ya dauke shi. Juyowa na yi na kalli kwanciyarsa, ina mamakin karfin hali irin na ďa namiji a haka kuma yake kallo muna ta rayuwa a gidan kamar babu komai a tsakaninsa da Hana. Sallah bata wani dame shi ba daman ni ce mai tashi da wuri na yi, dan haka na sauko da kafafuwana kasa na nufi bandaki, wanka na fara yi sannan na yi alwala na fito sanyin ruwan da kuma ac dakin yana ratsani sai ya saka na dan ji sassauci a jikina. Na zuciya kan na san har abada ba zan samu ba. Ni da farinciki mun yi bankwana. Doguwar riga na zuba na shimfida sallaya na sauke farali sannan na fara tasbihi. Ban daga sallayar ba har sai da na ji farkawarsa misalin bakwai na safe. “Miyasa ba ki tashe ni ba gashi rana ta yi” “Ni ma ban farka da wuri ba” Shi kawai na iya amsawa na koma saman gadon na kwanta na lafe kamar mai bachi, domin har lokacin ban san me zan yi ba. Na nuna musu an san komai na rufe su da fada ko kuma na danna na barwa zuciyata komai na bar su da Allah? Amman zan yi? Ina jin abun kamar ba shi da sauki, ina jin zaba da radadin cin amanar da yar'uwata ta yi min fiye da kunar garwashin wuta. Ina jin da ya taba ni yana fadin. “My soul ta so muje mu yo breakfast” “Sai anjima bana son komai yanzu” Na amsa hawaye na min zuba yayin da fuskata take lullube a cikin bargo. “Okay, ba ki da lafiya ne?” “Lafiya kalau bana son damuwa dan Allah ka tafi” “Okay.. I'm sorry dear...” Ya fice daga dakin sai after like 40m ya dawo yayi shirin office. “Bachin be ishe ki ba kenan? Ni zan wuce aiki sai na dawo” Bance masa komai har ya fita. Sannan na tashi zaune gaba daya na rasa me zan yi kaina ya daure abun yayi min muni. Sauka na yi saman gadon na fito falo na nufi windows ya na daga curtain ina kallon motar da Abdull ya shiga Hana kuma ta bude front seat ta shiga ta zauna. Hawaye ya sauko min a haka suke kallona? Yar'uwata ta zama kishiyata ta san sirrina ta san komai akan mijina. Kusan a falon na wuni ina ta yawo ya kasa sukuni na rasa kalar tunanin da zan yi, kamin na samu natsuwar yankewa kaina shawarar da nake ganin ta dace da ni. Bayan ruwa ban iya sha ko cin komai ba har karfe biyu ta yi na rana na je na yi sallah na fito falo na zauna ina jiran dawowar Hana, domin ita ce mai dawowa da wuri Abdull sai biyar ko shida yake dawowa gidan. Na bata awa daya a zaune sannan ta turo kofar falon ta shigo da sallama na amsa mata ba tare da na bari ta kalli ido na. Domin na yi kuka har idon ya kumbura, kai tsaye ta wuce dakinta, kaya kawai ta canja ta fito ta nufi kitchen kamar yadda ta saba sai na bi da kallo wai yanzu ita ma tana dauke da ciki kamar yadda nake dauke da shi kuma cikin mutum daya. Sai da ta shiga ta kunna gas ta dora ruwan zafi sannan ta tambaye daga can kitchen din. “Noor me za a dora” Na mike tsaye na nufi kitchen din na shiga, sai na zame ta tana yanka lemu zata sha sai dai gani na ya saka ta tsayar da yankan da take. “Lafiya? Me ya samu idonki?” “Kuka na yi” Ta aje lemun da wukar ta matso kusa da ni. “Kuka dai? Fada kuka yi da Ya Abdull ne ko baki da Lafiya?” Na kalleta ina mamakin yadda take nuna min kulawa kamar ba zata ci amanata a bayan idona ba. “Na san muna samun tsabani Hana, amman ina sonki ina sonki sosai, zuciyata bata taba raya min na cutar da ke ba, ni ba zan iya?” “Me ya kawo wannan maganar Noor?” “Ina tunanar da ke ne idan kin manta, Wallahi Hana ko rayuwata kika ce kina so zan iya baki, balle mijina zan iya mallaka miki Abdull mallakawa ta har abada Hana, Wallahi zan iya yin duk yadda zan yi na ga ya sake ni in ya so sai ki aureshi” Ta matsa baya tana kallona cikin tashin hankalin da ya bayyana a fuskarta. “Me Abdull ya fada miki? Wallahi sheri yayi min” “Babu wanda ya fada min komai, ni na ji da kunena, na kuma gani da idona, kika hada kai da mijina yana ba ni maganin bachi saboda yayi tarayya dake” Ta daga hannu biyu tana yi min rantsuwa. “Wallahi Wallahi Wallahi Noor ban hada kai da shi ba?” Na daka mata tsawa. “To me yake zuwa yi dakinki? Kullum sai ya ba ni maganin bachi na sha sannan ya tafi dakinki kishiyata ce ke?” Ta girgiza kai tana kuka. “Aa amman ba yadda kika tunani ba ne, Wallahi ni ban ci amanarki ba, Wallahi Noor ba son raina ba ne” “Haka ne, shiyasa ai yake tafiya dakinki har kuna hira kina tambayarsa yaushe za a zubar da ciki, ina dauke da cikinsa kina dauke da cikinsa wane irin wulakanci da kaskaanci ne wannan?” Ta zube kasan guiwoyinta tana kuka. “Na shiga uku dan Allah Noor ki yi hakuri ki fahimce ni” “Wace fahimta zan miki wanda ta wuce wannan? Ko karya nake baki dauke da cikin Abdull ba ki tarayya da shi?” “Gaskiya ne ina dauke da cikin ina tarayya da shi, amman ba ta yadda kike tunani ba ne, ina son dan Allah ki fahimce ni” “Toh ina jinki fahimtar da ni” Ta kasa magana sai kuka take daman ai ba zata iya magana ba, tun da bata da kalaman da zata wanke kanta da su a gurina. “Tun yaushe kuke cin amanata?” Nan ma ta kasa magana, sai na matsa kusa da ita na tabbatar mata da abun da shi ne tabbbatacce a zuciyata. “Na bar miki Abdull har abada, na bar miki Hana, yau ba zan kwana da aurensa ba” Na wuce na shige dakina na fada kan gadona ina kuka mai karfi. Abincin da bata girka ba kenan ni kuma ban sake fita dakin ba sai da na ji motar Abdull. Tsanar hada ido da shi ne ta saka na fice daga dakin na nufi kitchen na tsaya a cikin har ya shigo. “Bacchi kuke ne?” Na ji ya fada domin yayi sallama be ji kowa ya amsa masa ba. Sai da na tabbatar ya shiga dakin, sannan na fito kitchen din. Dakin da Hana take na shiga na nufi gurin da takardunta suke na bude jakarta na dauko littafi na cire paper na dauki pen, sannan na kalli kofar bandakinta da nake jiyo kukanta na munafurci daman na san haka zata yi ai, karshen munafuki jin kunya. Na shiga da kuzarina, domin na gama yanke shawara Wallahi ko auren Abdull ne rayuwata yau kam na shiryawa mutuwa domin ba zan iya kara awa daya da aurensa ba. Zaune na same shi sanye da suit dinsa na aiki da be cire ba yana duba wayarsa da alama wani abun yake kallo. A lokacin da na kalli fuskarsa sai na ji ban taba tsanar kowa a duniya kamar yadda nake jin tsanarsa ba. Kusa da shi na karasa na aje masa takardar da biron. Ya kalli takardar da biron da na aje masa. “Miye wannan?” “Me ka gani?” Na tambaya ina kallonsa cike da tsana da kyama. “Takardar da biro” “So na nake ka rubuta min saki” Ya kalleni. “Are you okay?” “Ka ji ni ai i mean it ka rubuta min saki na ce!!!” Na karashe zance a tsawace. Ya aje wayar hannunsa ya mike tsaye. “Saki? My soul kin san me kike fada kuwa? Ba a wasa da wannan kalmar fa” Ya dafa ni sai na buge hannunsa ina tauna hakora ta cikin bakina. “Wani abu kika sha yau?” “Eh... Na sha bala'i da masifa da wutar da zan amayar maka a yanzu nan idan baka sake ni ba” “Na sake ki kamar yaya me yake damunki?” “Kai ne kai kake damuna Abdullahi, na tsane ka, damba marar tunani dan duniya wulakantacce, barikin ta wuce waje har sai ta shigo cikin gidana? Sai ka hurumina da yar'uwata?” “Kina da hankali kuwa? Ni kike kira damba...” Ya daga hannu zai mare ni, a nan Allah ya ba ni iko da karfin iya rike hannun da dukanin karfina. “Maci amana, karka sake tsinanen hannunka ya kai ga halattaciyar fuskata ma ci amana ka bi yaya ka bi kanwarta, haihuwar hasara” “Okay ta kwashe karya da gaskiya ta fada miki kin zo kina zargina da abun da ban aikata ba ko? Saboda tsaurin ido har ki kalleni kina kirana da suna kala kala ko? Ni fa mijinki Noor” Na tofa masa yawu a fuska. “Allah ya kiyaye Allah ya kiyaye yanzu kam, da can amman ban da yanzu” “Okay rashin kunya zaki nuna min ko? To sai na ga idan akwai uban da ya isa ya saka na sake ki, kuma kika sake fada min wata maganar banza sai na ci ubanki yanzu nan” “Ubana yayi maka yawa, kuma babu wanda zai saka kaka kai zaka sake ni dan kanka, wato kai da yake namiji mai karfin hali dan duniya har kana da bakin yakata ko? Taya zaka ba ni maganin bachi ka tafi ko wane dare ka kwanta da yar'uwata sai asuba ka dawo ku ci amanata a tare kuma ka ce ba zaka sake ni ba? Wallahi karya kake Abdullahi” Ya nuna kansa yana murje ido kamar da gaske be aikata ba. “Ni nake saka miki maganin bachi?” “Aa ni nake sakawa kaina, wanda ka ba ni jiya ya zube ban sha ba, ina kallon lokacin da ka tashi daga dakin nan ka tafi dakin Hana, na labe na ji abun da kuke magana a kai, har ciki za ku zubar” Na fashe da kuka domin ba ni da wani abun yi a yanzu kamar shi. “Ba laifinka ba ne, laifin yar'uwata ne ita da ta ci amanata, dama kum jira wata kila gurin haihu zan mutu ai sai ka aureta ku zauna” “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Ya sassauta muryarsa. “Noor Wallahi aikin sheidan ne, kuskure ne aka samu, me Hana ta fada miki?” “Ban saurareta ba, kamar yadda ba zan saurareka ba, saki kawai nake so ka sake ni” “Ni ba zan sake ki ba Ina son ki Noor shedan ne Wallahi” Kalmar ina son ki ta saka na ji kamar da wuka a kusa na daka masa a sautin zuciya. Ya matso kusa da ni “Abu ne da zamu tsaya mu rufawa juna asiri, ita yar'uwarki ce ni kuma mijinki ne, kuma ga cikina a jikinki Noor, Wallahi na miki alkawari ba zan sake ba” “Gobe zan tafi na bar muku gidan, ku cigaba da aikata abun da kuke har mahadi ya bayyana, ni dai ka sake ni” “Ba zan sake ki ba Noor ni ba zan sake ki ba, ni ban taba aikata komai ba sai a wannan karon da Allah ya kawo tsautsayi” “Karya kake, ba wannan ne karon farko ba Wallahi kawai dai ban gane ba sai yanzu, shiyasa tun kamin ka aure ni kake ta taba ni, da na yi magana ka ce gwada ni kake yi, ashe gwadawa kake ka gani idan ni yar iska ce na amince maka a waje, ka gama da ni ka tafi, da hakan be samu sai ka bijiro da maganar aure, da na samu ciki kuma sai na daina burge ka saboda ba auren Allah ba ne, auren sha'awa ka yi min. Sai kuma sha'awarka ta koma gurin kanwata jinina, ita kuma bata duba alaka ba ta yarda kuka taru kuka ci amanata” Na dafe zuciyata ina bakincin da ban fahimci wannan red flag din ba tun farko, ga kuma Safeena ma ai izina ce. Ya dafe kansa ya juya ya juyo ya fara safa da marwa kamin ya samu tsayawa gabana a rikece har da fashe min da kuka. “Dan Allah ki kwantar da hankalinki mu yi magana ta fahimta, sakinki zai bata abubuwa ne kawai, ina zaki je da ciki? Abun nan aikin shaidan ne Noor zai iya fadawa kan kowa, zan tafi na bar miki gidan har hankalinki ya kwanta amman ni ba zan sake ki ba” A take kukan ya yanke min. “Ba zaka sake ni ba saboda kana tsoron kar a tambayi dalilin mutuwar na fadi cewar kai da yar'uwata kuka ci amanata?” Yayi kamar be ji ba dauki wayarsa yana kuka zai fice dakin. “Ba zaka sake ni ba, sai na hada maka cewar dan da Safeena ta haifa maka yanzu ba jininka ba ne, ďan falkanta ne, ex-boyfriend dinta? Sai na fada maka dalilin da ya saka Safeena ta daina daga maka hankali akan aurena? Sai na fada maka na san Safeena irin wanin da baka yi mata ba? Sai na fada maka a duk lokacin da ka bar Kano tana tarayya da Ex dinta ne har sai ka dawo? Sai na fada maka Safeena ta taba ji min ciwo a hannu saboda ta yi tunanin Ex dinta kuma falkamta so na yake, saboda kishinsa?” Ya juyo ya kalleni kukan da yake ya tsaya. “Kina cikin bachin rai ne, zaki iya fadar komai Noor na sani” “Ina cikin bacin rai, amman ba cikin gushewar hankali ba, idan baka yarda ba ka dauki yaron ka gwada jininsa da naka mana, ka cancanci haka ai, daman shege sai dan iska, a da har mamakin dalilin Safeena nake na aikata haka, ashe ta yi daidaita kai din tsohon shege ne” Ya daka min tsawa. “Ya ishe ki haka yanzu kam ya ishe ki haka? Mace nawa take kama mijinta yana abun da be dace ba amman ta rufa masa asiri a zaune, balle ni da kaddara ce kuma ba ni kadai ba har da yar'uwarki, kusan ma ita ta ja ra'ayi a komai” “Wallahi ko kai ne dan autan maza na gama zaman aure da kai Abdull, ko ka sake ni ko na daga na kira uwarka a yanzu na fada mata abun da ka aikata da kanwata kuma na tabbatar mata cewar ďan da Safeena take shayarwa a yanzu ba jikanta ba ne? Domin ba jininka ba ne, na yarda idan aka bincika aka tararda tsabanin haka a kai ni kotu, ko dai so kake na kira kanenka da mahaifiyata ma fada musu? Kwanciyar hankalinka ka sake ni, Ba zan fadawa kowa abun da kuka aikata ba ni na bar ku da Allah” A fusace ya nufi takardar ya dauka yayi rubutu a kai ya jefa min a fuska. “Ke ce da bakinciki ba ni ba...” Ya nufi kofa. “Allah ya raba ni da bakinciki tun da ya raba ni da kai” Na fashe da kuka mai karfi. Na yi kuka kuka sosai kuka irin na macen da rauni ya mamayeta ta rasa makoma, saki nake so kuma na samu yanzu idan na koma gida me zan fadawa iyayenmu? Na fada cikina ina bakinciki da ban zaba masa uba na gari ba. A dakin na kwana, sai dai bachi be dauke ni ba, bayan ruwa bana shan komai ba, shi kuma tun da ya fita be dawo ba, har garin Allah ya waye. Cikin kuka da bakinciki na yi sallah Asuba, na roki Allah ya sanyaya min zuciyata ya sanya min saka min kana'a domin har lokacin ban ji zan iya yi ma yar'uwata wata bakar addu'a ba, har gobe ita din jini na ce idan wani abun ya faru da ita kamar ya faru da ni ne. Ni dai na san na barta da Allah shi ya san abun da ya dace da ita kuma shi ya san sakamakon da zai yi min akanta. Misalin shida da rabi na fara hada kayana cikin akwaiti sai da na yi nisa da hadawa sai kuma, sai kuma na ji bana bukatar kala ko daya domin Abdull ne ya siya, a yanzu kuma bana sha'awar duk wani abu mai alaka da shi. Cikinsa ma da yake jikina da ace zan iya da cire shi zan yi na aje masa a gidansa na yi tafiyata. Jaka kawai na nufa na dauka na hada yan kudadena na dauki wayata ita ma dan ta zame min dole a yanzu. Hijabi na saka sannan na dauki takardar sakin da ban iya karantawa ba na saka a jaka na nufi kofar dakin na bude, sai na yi arba da doguwar takardar aje a kofar daki. Na duka na saka hannu na dauka a tunani Abdull ne ya aje min amman da na fara karantawa sai na tararda sabanin haka.. _Yar uwata noor, ban ci amanarki, ba zan taba iya cin amanarki ba, ba ki saurare ni ba, bakinciki be bari kin tuna da halina ba! Yadda kika dauki abun ba haka yake ba, Wallahi mijinki ya nuna min fin karfi ne, ya fara tallata min bukatarsa tun a lokacin da na bukaci tafiya gida kika hanani ne. A lokacin bana son fada miki ne saboda kar na zama silar lalacewar aurenki..._ Na hade yawu na nufi kujera na zauna. _Da ya fahimci ba zan aminta ba, sai ya shirya min tarko, ranar Monday da muka fita da sunan zai sauke ni a hanya, sai ya biya da ni a wata tsohuwar ma'aikatarsu, yace min zai tafi ya duba wani abun ne, ban yi tunanin zai nuna min karfi ba ne, shiyasa ta yace na shiga wani office na dan jira shi, na jira har na gaji da zama be dawo ba da na fito sai na lura gurin babu mutane sosai, na tsorata da farko na dauka siyar da ni zai yi, ashe kudirinsa dabam ne. Na koma ciki na zauna jiransa har ya dawo, sai ya fara lallaba ni yana min kamfe da abubuwan da yake min na kyautatawa ashe ba dan Allah yayi min ba, da na nuna masa ba haka ya fara kokawa da ni, Wallahi na yi ina yadda zan iya na kare kaina Noor amman hakan be samu ba sai da ya biya bukatarsa, a ranar ban samu tafiya makaranta ba a gurin na wuni, sai da ya dawo aiki ya biyo ya dauke ni aje ni nesa da gidan na tako na iso da kafa sannan ya shigo_ Hawayena sun zuba jikin takardar na juya dayan shafin ina karantawa. _Daga ranar ne ciki ya shige ni, tun daga lokacin yake bibiyata yana ba ni hakuri kuma yana lallaba ni ko zan amince amman ban amince masa ba, ba zan iya fada miki ba ne, saboda kar na zama silar lalacewar aurenki da na Mama na rumgumi a abun a matsayin kaddara. Shi da kansa ya ba ni abun auna ciki ya ce na auna idan babu ciki saboda kar mu ya bayyana mu ji kunya, kuma da na auna sai na samu akwai ciki amman ban san ko wata nawa ba ne, da na fada masa sai yace za a zubar amman sai na amince masa ya ci gaba da mu'alama da ni, da hakan ya ribance ni na amince saboda ina son a cire cikin kar ki gane, domin ya fada min ya san duk yadda zai yi ya wanke kansa ni ya bar ni a ruwa idan ban aminta ba, kuma gaskiya ya fada ni mace ce bayyanar cikin zai rusa rayuwata, shi kuma namiji ne, wanda ya riga ya gina rayuwarsa kaddarata bata isa ruguza komai ba_ Ya share hawayena ina kuka. _Ki yi tunani mana Noor yadda dangi da iyaye suke murna da dan halak, haka suke bakinciki da na haram, na san Baba kashe ni zai yi idan ya sani, buri na yadda za a zubar da ciki ne ba tare da kowa ya ji ba. Kullum maganar da nake masa kenan kuma saboda haka nake amincewa da shi, shi kuma yana ga jan lokaci saboda biyan bukatarsa. Amman ni ba zan iya cin amanarki ba Noor zuciyata ba haka take ba, ba a mana wannan tarbiyarba, tsorona na lalacewar aurenki ne da na Mama, ba ki tsaya kin saurare ni ba, ban san ya zan miki bayani ba_ Na mike tsaye da sauri a lokacin da nake karanta sakonta na karshe. _A lokacin da zaki samu sakon nan ki karanta bana gidanki, na bar gidanki Noor, kuma ba gida zan tafi ba, ba zan kaiwa Mama abun kunya ba, ba zan tafi da cikin shege gidan Baba ba, na san zaki fada musu dukan abun da ya faru a lokacin da zaki koma gida ko kuma aka neme ni aka rasa. Dan Allah ki fada musu gaskiya Wallahi ba da son na aikata ba, kaddara ce ta riga fata, zan tafi inda ban san kowa ba kuma kowa be san ni ba, na bar ku Noor ku yafe ni, musamman ke...!_ Na jefar da takardar na nufi dakinta da sauri ina kiranta. “Hana Hana Hana...” Na tura sai na samu dakin babu kowa, na fada bandaki nan ma bata nan, na fito da gudu na nufo gate ina tambayar mai gadi ko ya ga fitarta. “Hana ai tun jiya da dare ta fita, misalin sha daya na dare” Na fashe da kuka na bude gate din na fita da gudu kamar ance zan ganta. Na yi dama na kalli karshen Titi da babu mutane na juyo na yi hagu nan ma babu alamar sawunta. A gurin na zube na kwarara wani irin ihu da dukan karfina ina kuka har sai da abun da ke cikina na motsa.... Duk wanda ta karanta min littafi bata biya ba na barta da ALLAH. duk wanda ta yi min sharing paid pages na barta da ALLAH. It's 500 Zenith Bank Hadiza Abubakar 2451879008 And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660Be dade da kwanciya ba na ji nishanrinsa alamar bachi mai nauyi ya dauke shi. Juyowa na yi na kalli kwanciyarsa, ina mamakin karfin hali irin na ďa namiji a haka kuma yake kallo muna ta rayuwa a gidan kamar babu komai a tsakaninsa da Hana. Sallah bata wani dame shi ba daman ni ce mai tashi da wuri na yi, dan haka na sauko da kafafuwana kasa na nufi bandaki, wanka na fara yi sannan na yi alwala na fito sanyin ruwan da kuma ac dakin yana ratsani sai ya saka na dan ji sassauci a jikina. Na zuciya kan na san har abada ba zan samu ba. Ni da farinciki mun yi bankwana. Doguwar riga na zuba na shimfida sallaya na sauke farali sannan na fara tasbihi. Ban daga sallayar ba har sai da na ji farkawarsa misalin bakwai na safe. “Miyasa ba ki tashe ni ba gashi rana ta yi” “Ni ma ban farka da wuri ba” Shi kawai na iya amsawa na koma saman gadon na kwanta na lafe kamar mai bachi, domin har lokacin ban san me zan yi ba. Na nuna musu an san komai na rufe su da fada ko kuma na danna na barwa zuciyata komai na bar su da Allah? Amman zan yi? Ina jin abun kamar ba shi da sauki, ina jin zaba da radadin cin amanar da yar'uwata ta yi min fiye da kunar garwashin wuta. Ina jin da ya taba ni yana fadin. “My soul ta so muje mu yo breakfast” “Sai anjima bana son komai yanzu” Na amsa hawaye na min zuba yayin da fuskata take lullube a cikin bargo. “Okay, ba ki da lafiya ne?” “Lafiya kalau bana son damuwa dan Allah ka tafi” “Okay.. I'm sorry dear...” Ya fice daga dakin sai after like 40m ya dawo yayi shirin office. “Bachin be ishe ki ba kenan? Ni zan wuce aiki sai na dawo” Bance masa komai har ya fita. Sannan na tashi zaune gaba daya na rasa me zan yi kaina ya daure abun yayi min muni. Sauka na yi saman gadon na fito falo na nufi windows ya na daga curtain ina kallon motar da Abdull ya shiga Hana kuma ta bude front seat ta shiga ta zauna. Hawaye ya sauko min a haka suke kallona? Yar'uwata ta zama kishiyata ta san sirrina ta san komai akan mijina. Kusan a falon na wuni ina ta yawo ya kasa sukuni na rasa kalar tunanin da zan yi, kamin na samu natsuwar yankewa kaina shawarar da nake ganin ta dace da ni. Bayan ruwa ban iya sha ko cin komai ba har karfe biyu ta yi na rana na je na yi sallah na fito falo na zauna ina jiran dawowar Hana, domin ita ce mai dawowa da wuri Abdull sai biyar ko shida yake dawowa gidan. Na bata awa daya a zaune sannan ta turo kofar falon ta shigo da sallama na amsa mata ba tare da na bari ta kalli ido na. Domin na yi kuka har idon ya kumbura, kai tsaye ta wuce dakinta, kaya kawai ta canja ta fito ta nufi kitchen kamar yadda ta saba sai na bi da kallo wai yanzu ita ma tana dauke da ciki kamar yadda nake dauke da shi kuma cikin mutum daya. Sai da ta shiga ta kunna gas ta dora ruwan zafi sannan ta tambaye daga can kitchen din. “Noor me za a dora” Na mike tsaye na nufi kitchen din na shiga, sai na zame ta tana yanka lemu zata sha sai dai gani na ya saka ta tsayar da yankan da take. “Lafiya? Me ya samu idonki?” “Kuka na yi” Ta aje lemun da wukar ta matso kusa da ni. “Kuka dai? Fada kuka yi da Ya Abdull ne ko baki da Lafiya?” Na kalleta ina mamakin yadda take nuna min kulawa kamar ba zata ci amanata a bayan idona ba. “Na san muna samun tsabani Hana, amman ina sonki ina sonki sosai, zuciyata bata taba raya min na cutar da ke ba, ni ba zan iya?” “Me ya kawo wannan maganar Noor?” “Ina tunanar da ke ne idan kin manta, Wallahi Hana ko rayuwata kika ce kina so zan iya baki, balle mijina zan iya mallaka miki Abdull mallakawa ta har abada Hana, Wallahi zan iya yin duk yadda zan yi na ga ya sake ni in ya so sai ki aureshi” Ta matsa baya tana kallona cikin tashin hankalin da ya bayyana a fuskarta. “Me Abdull ya fada miki? Wallahi sheri yayi min” “Babu wanda ya fada min komai, ni na ji da kunena, na kuma gani da idona, kika hada kai da mijina yana ba ni maganin bachi saboda yayi tarayya dake” Ta daga hannu biyu tana yi min rantsuwa. “Wallahi Wallahi Wallahi Noor ban hada kai da shi ba?” Na daka mata tsawa. “To me yake zuwa yi dakinki? Kullum sai ya ba ni maganin bachi na sha sannan ya tafi dakinki kishiyata ce ke?” Ta girgiza kai tana kuka. “Aa amman ba yadda kika tunani ba ne, Wallahi ni ban ci amanarki ba, Wallahi Noor ba son raina ba ne” “Haka ne, shiyasa ai yake tafiya dakinki har kuna hira kina tambayarsa yaushe za a zubar da ciki, ina dauke da cikinsa kina dauke da cikinsa wane irin wulakanci da kaskaanci ne wannan?” Ta zube kasan guiwoyinta tana kuka. “Na shiga uku dan Allah Noor ki yi hakuri ki fahimce ni” “Wace fahimta zan miki wanda ta wuce wannan? Ko karya nake baki dauke da cikin Abdull ba ki tarayya da shi?” “Gaskiya ne ina dauke da cikin ina tarayya da shi, amman ba ta yadda kike tunani ba ne, ina son dan Allah ki fahimce ni” “Toh ina jinki fahimtar da ni” Ta kasa magana sai kuka take daman ai ba zata iya magana ba, tun da bata da kalaman da zata wanke kanta da su a gurina. “Tun yaushe kuke cin amanata?” Nan ma ta kasa magana, sai na matsa kusa da ita na tabbatar mata da abun da shi ne tabbbatacce a zuciyata. “Na bar miki Abdull har abada, na bar miki Hana, yau ba zan kwana da aurensa ba” Na wuce na shige dakina na fada kan gadona ina kuka mai karfi. Abincin da bata girka ba kenan ni kuma ban sake fita dakin ba sai da na ji motar Abdull. Tsanar hada ido da shi ne ta saka na fice daga dakin na nufi kitchen na tsaya a cikin har ya shigo. “Bacchi kuke ne?” Na ji ya fada domin yayi sallama be ji kowa ya amsa masa ba. Sai da na tabbatar ya shiga dakin, sannan na fito kitchen din. Dakin da Hana take na shiga na nufi gurin da takardunta suke na bude jakarta na dauko littafi na cire paper na dauki pen, sannan na kalli kofar bandakinta da nake jiyo kukanta na munafurci daman na san haka zata yi ai, karshen munafuki jin kunya. Na shiga da kuzarina, domin na gama yanke shawara Wallahi ko auren Abdull ne rayuwata yau kam na shiryawa mutuwa domin ba zan iya kara awa daya da aurensa ba. Zaune na same shi sanye da suit dinsa na aiki da be cire ba yana duba wayarsa da alama wani abun yake kallo. A lokacin da na kalli fuskarsa sai na ji ban taba tsanar kowa a duniya kamar yadda nake jin tsanarsa ba. Kusa da shi na karasa na aje masa takardar da biron. Ya kalli takardar da biron da na aje masa. “Miye wannan?” “Me ka gani?” Na tambaya ina kallonsa cike da tsana da kyama. “Takardar da biro” “So na nake ka rubuta min saki” Ya kalleni. “Are you okay?” “Ka ji ni ai i mean it ka rubuta min saki na ce!!!” Na karashe zance a tsawace. Ya aje wayar hannunsa ya mike tsaye. “Saki? My soul kin san me kike fada kuwa? Ba a wasa da wannan kalmar fa” Ya dafa ni sai na buge hannunsa ina tauna hakora ta cikin bakina. “Wani abu kika sha yau?” “Eh... Na sha bala'i da masifa da wutar da zan amayar maka a yanzu nan idan baka sake ni ba” “Na sake ki kamar yaya me yake damunki?” “Kai ne kai kake damuna Abdullahi, na tsane ka, damba marar tunani dan duniya wulakantacce, barikin ta wuce waje har sai ta shigo cikin gidana? Sai ka hurumina da yar'uwata?” “Kina da hankali kuwa? Ni kike kira damba...” Ya daga hannu zai mare ni, a nan Allah ya ba ni iko da karfin iya rike hannun da dukanin karfina. “Maci amana, karka sake tsinanen hannunka ya kai ga halattaciyar fuskata ma ci amana ka bi yaya ka bi kanwarta, haihuwar hasara” “Okay ta kwashe karya da gaskiya ta fada miki kin zo kina zargina da abun da ban aikata ba ko? Saboda tsaurin ido har ki kalleni kina kirana da suna kala kala ko? Ni fa mijinki Noor” Na tofa masa yawu a fuska. “Allah ya kiyaye Allah ya kiyaye yanzu kam, da can amman ban da yanzu” “Okay rashin kunya zaki nuna min ko? To sai na ga idan akwai uban da ya isa ya saka na sake ki, kuma kika sake fada min wata maganar banza sai na ci ubanki yanzu nan” “Ubana yayi maka yawa, kuma babu wanda zai saka kaka kai zaka sake ni dan kanka, wato kai da yake namiji mai karfin hali dan duniya har kana da bakin yakata ko? Taya zaka ba ni maganin bachi ka tafi ko wane dare ka kwanta da yar'uwata sai asuba ka dawo ku ci amanata a tare kuma ka ce ba zaka sake ni ba? Wallahi karya kake Abdullahi” Ya nuna kansa yana murje ido kamar da gaske be aikata ba. “Ni nake saka miki maganin bachi?” “Aa ni nake sakawa kaina, wanda ka ba ni jiya ya zube ban sha ba, ina kallon lokacin da ka tashi daga dakin nan ka tafi dakin Hana, na labe na ji abun da kuke magana a kai, har ciki za ku zubar” Na fashe da kuka domin ba ni da wani abun yi a yanzu kamar shi. “Ba laifinka ba ne, laifin yar'uwata ne ita da ta ci amanata, dama kum jira wata kila gurin haihu zan mutu ai sai ka aureta ku zauna” “Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un” Ya sassauta muryarsa. “Noor Wallahi aikin sheidan ne, kuskure ne aka samu, me Hana ta fada miki?” “Ban saurareta ba, kamar yadda ba zan saurareka ba, saki kawai nake so ka sake ni” “Ni ba zan sake ki ba Ina son ki Noor shedan ne Wallahi” Kalmar ina son ki ta saka na ji kamar da wuka a kusa na daka masa a sautin zuciya. Ya matso kusa da ni “Abu ne da zamu tsaya mu rufawa juna asiri, ita yar'uwarki ce ni kuma mijinki ne, kuma ga cikina a jikinki Noor, Wallahi na miki alkawari ba zan sake ba” “Gobe zan tafi na bar muku gidan, ku cigaba da aikata abun da kuke har mahadi ya bayyana, ni dai ka sake ni” “Ba zan sake ki ba Noor ni ba zan sake ki ba, ni ban taba aikata komai ba sai a wannan karon da Allah ya kawo tsautsayi” “Karya kake, ba wannan ne karon farko ba Wallahi kawai dai ban gane ba sai yanzu, shiyasa tun kamin ka aure ni kake ta taba ni, da na yi magana ka ce gwada ni kake yi, ashe gwadawa kake ka gani idan ni yar iska ce na amince maka a waje, ka gama da ni ka tafi, da hakan be samu sai ka bijiro da maganar aure, da na samu ciki kuma sai na daina burge ka saboda ba auren Allah ba ne, auren sha'awa ka yi min. Sai kuma sha'awarka ta koma gurin kanwata jinina, ita kuma bata duba alaka ba ta yarda kuka taru kuka ci amanata” Na dafe zuciyata ina bakincin da ban fahimci wannan red flag din ba tun farko, ga kuma Safeena ma ai izina ce. Ya dafe kansa ya juya ya juyo ya fara safa da marwa kamin ya samu tsayawa gabana a rikece har da fashe min da kuka. “Dan Allah ki kwantar da hankalinki mu yi magana ta fahimta, sakinki zai bata abubuwa ne kawai, ina zaki je da ciki? Abun nan aikin shaidan ne Noor zai iya fadawa kan kowa, zan tafi na bar miki gidan har hankalinki ya kwanta amman ni ba zan sake ki ba” A take kukan ya yanke min. “Ba zaka sake ni ba saboda kana tsoron kar a tambayi dalilin mutuwar na fadi cewar kai da yar'uwata kuka ci amanata?” Yayi kamar be ji ba dauki wayarsa yana kuka zai fice dakin. “Ba zaka sake ni ba, sai na hada maka cewar dan da Safeena ta haifa maka yanzu ba jininka ba ne, ďan falkanta ne, ex-boyfriend dinta? Sai na fada maka dalilin da ya saka Safeena ta daina daga maka hankali akan aurena? Sai na fada maka na san Safeena irin wanin da baka yi mata ba? Sai na fada maka a duk lokacin da ka bar Kano tana tarayya da Ex dinta ne har sai ka dawo? Sai na fada maka Safeena ta taba ji min ciwo a hannu saboda ta yi tunanin Ex dinta kuma falkamta so na yake, saboda kishinsa?” Ya juyo ya kalleni kukan da yake ya tsaya. “Kina cikin bachin rai ne, zaki iya fadar komai Noor na sani” “Ina cikin bacin rai, amman ba cikin gushewar hankali ba, idan baka yarda ba ka dauki yaron ka gwada jininsa da naka mana, ka cancanci haka ai, daman shege sai dan iska, a da har mamakin dalilin Safeena nake na aikata haka, ashe ta yi daidaita kai din tsohon shege ne” Ya daka min tsawa. “Ya ishe ki haka yanzu kam ya ishe ki haka? Mace nawa take kama mijinta yana abun da be dace ba amman ta rufa masa asiri a zaune, balle ni da kaddara ce kuma ba ni kadai ba har da yar'uwarki, kusan ma ita ta ja ra'ayi a komai” “Wallahi ko kai ne dan autan maza na gama zaman aure da kai Abdull, ko ka sake ni ko na daga na kira uwarka a yanzu na fada mata abun da ka aikata da kanwata kuma na tabbatar mata cewar ďan da Safeena take shayarwa a yanzu ba jikanta ba ne? Domin ba jininka ba ne, na yarda idan aka bincika aka tararda tsabanin haka a kai ni kotu, ko dai so kake na kira kanenka da mahaifiyata ma fada musu? Kwanciyar hankalinka ka sake ni, Ba zan fadawa kowa abun da kuka aikata ba ni na bar ku da Allah” A fusace ya nufi takardar ya dauka yayi rubutu a kai ya jefa min a fuska. “Ke ce da bakinciki ba ni ba...” Ya nufi kofa. “Allah ya raba ni da bakinciki tun da ya raba ni da kai” Na fashe da kuka mai karfi. Na yi kuka kuka sosai kuka irin na macen da rauni ya mamayeta ta rasa makoma, saki nake so kuma na samu yanzu idan na koma gida me zan fadawa iyayenmu? Na fada cikina ina bakinciki da ban zaba masa uba na gari ba. A dakin na kwana, sai dai bachi be dauke ni ba, bayan ruwa bana shan komai ba, shi kuma tun da ya fita be dawo ba, har garin Allah ya waye. Cikin kuka da bakinciki na yi sallah Asuba, na roki Allah ya sanyaya min zuciyata ya sanya min saka min kana'a domin har lokacin ban ji zan iya yi ma yar'uwata wata bakar addu'a ba, har gobe ita din jini na ce idan wani abun ya faru da ita kamar ya faru da ni ne. Ni dai na san na barta da Allah shi ya san abun da ya dace da ita kuma shi ya san sakamakon da zai yi min akanta. Misalin shida da rabi na fara hada kayana cikin akwaiti sai da na yi nisa da hadawa sai kuma, sai kuma na ji bana bukatar kala ko daya domin Abdull ne ya siya, a yanzu kuma bana sha'awar duk wani abu mai alaka da shi. Cikinsa ma da yake jikina da ace zan iya da cire shi zan yi na aje masa a gidansa na yi tafiyata. Jaka kawai na nufa na dauka na hada yan kudadena na dauki wayata ita ma dan ta zame min dole a yanzu. Hijabi na saka sannan na dauki takardar sakin da ban iya karantawa ba na saka a jaka na nufi kofar dakin na bude, sai na yi arba da doguwar takardar aje a kofar daki. Na duka na saka hannu na dauka a tunani Abdull ne ya aje min amman da na fara karantawa sai na tararda sabanin haka.. _Yar uwata noor, ban ci amanarki, ba zan taba iya cin amanarki ba, ba ki saurare ni ba, bakinciki be bari kin tuna da halina ba! Yadda kika dauki abun ba haka yake ba, Wallahi mijinki ya nuna min fin karfi ne, ya fara tallata min bukatarsa tun a lokacin da na bukaci tafiya gida kika hanani ne. A lokacin bana son fada miki ne saboda kar na zama silar lalacewar aurenki..._ Na hade yawu na nufi kujera na zauna. _Da ya fahimci ba zan aminta ba, sai ya shirya min tarko, ranar Monday da muka fita da sunan zai sauke ni a hanya, sai ya biya da ni a wata tsohuwar ma'aikatarsu, yace min zai tafi ya duba wani abun ne, ban yi tunanin zai nuna min karfi ba ne, shiyasa ta yace na shiga wani office na dan jira shi, na jira har na gaji da zama be dawo ba da na fito sai na lura gurin babu mutane sosai, na tsorata da farko na dauka siyar da ni zai yi, ashe kudirinsa dabam ne. Na koma ciki na zauna jiransa har ya dawo, sai ya fara lallaba ni yana min kamfe da abubuwan da yake min na kyautatawa ashe ba dan Allah yayi min ba, da na nuna masa ba haka ya fara kokawa da ni, Wallahi na yi ina yadda zan iya na kare kaina Noor amman hakan be samu ba sai da ya biya bukatarsa, a ranar ban samu tafiya makaranta ba a gurin na wuni, sai da ya dawo aiki ya biyo ya dauke ni aje ni nesa da gidan na tako na iso da kafa sannan ya shigo_ Hawayena sun zuba jikin takardar na juya dayan shafin ina karantawa. _Daga ranar ne ciki ya shige ni, tun daga lokacin yake bibiyata yana ba ni hakuri kuma yana lallaba ni ko zan amince amman ban amince masa ba, ba zan iya fada miki ba ne, saboda kar na zama silar lalacewar aurenki da na Mama na rumgumi a abun a matsayin kaddara. Shi da kansa ya ba ni abun auna ciki ya ce na auna idan babu ciki saboda kar mu ya bayyana mu ji kunya, kuma da na auna sai na samu akwai ciki amman ban san ko wata nawa ba ne, da na fada masa sai yace za a zubar amman sai na amince masa ya ci gaba da mu'alama da ni, da hakan ya ribance ni na amince saboda ina son a cire cikin kar ki gane, domin ya fada min ya san duk yadda zai yi ya wanke kansa ni ya bar ni a ruwa idan ban aminta ba, kuma gaskiya ya fada ni mace ce bayyanar cikin zai rusa rayuwata, shi kuma namiji ne, wanda ya riga ya gina rayuwarsa kaddarata bata isa ruguza komai ba_ Ya share hawayena ina kuka. _Ki yi tunani mana Noor yadda dangi da iyaye suke murna da dan halak, haka suke bakinciki da na haram, na san Baba kashe ni zai yi idan ya sani, buri na yadda za a zubar da ciki ne ba tare da kowa ya ji ba. Kullum maganar da nake masa kenan kuma saboda haka nake amincewa da shi, shi kuma yana ga jan lokaci saboda biyan bukatarsa. Amman ni ba zan iya cin amanarki ba Noor zuciyata ba haka take ba, ba a mana wannan tarbiyarba, tsorona na lalacewar aurenki ne da na Mama, ba ki tsaya kin saurare ni ba, ban san ya zan miki bayani ba_ Na mike tsaye da sauri a lokacin da nake karanta sakonta na karshe. _A lokacin da zaki samu sakon nan ki karanta bana gidanki, na bar gidanki Noor, kuma ba gida zan tafi ba, ba zan kaiwa Mama abun kunya ba, ba zan tafi da cikin shege gidan Baba ba, na san zaki fada musu dukan abun da ya faru a lokacin da zaki koma gida ko kuma aka neme ni aka rasa. Dan Allah ki fada musu gaskiya Wallahi ba da son na aikata ba, kaddara ce ta riga fata, zan tafi inda ban san kowa ba kuma kowa be san ni ba, na bar ku Noor ku yafe ni, musamman ke...!_ Na jefar da takardar na nufi dakinta da sauri ina kiranta. “Hana Hana Hana...” Na tura sai na samu dakin babu kowa, na fada bandaki nan ma bata nan, na fito da gudu na nufo gate ina tambayar mai gadi ko ya ga fitarta. “Hana ai tun jiya da dare ta fita, misalin sha daya na dare” Na fashe da kuka na bude gate din na fita da gudu kamar ance zan ganta. Na yi dama na kalli karshen Titi da babu mutane na juyo na yi hagu nan ma babu alamar sawunta. A gurin na zube na kwarara wani irin ihu da dukan karfina ina kuka har sai da abun da ke cikina na motsa.... Duk wanda ta karanta min littafi bata biya ba na barta da ALLAH. duk wanda ta yi min sharing paid pages na barta da ALLAH. It's 500 Zenith Bank Hadiza Abubakar 2451879008 And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660Na dauki awa hudu ina nakudar da ban san da zuwanta sai da muka tafi asibiti, na wahala iya wahala har na yi zaton rai zai yi bankwana da duniya ne. Suka can na yi nishi na yunkura ina ta kokarina, amman kamar bana yi, ban yi zaton haka haihuwa take da da wahala da ciwon fa azaba ba sai da na kai matakin. A lokacin da likitoci suka bada shawarar a shiga ni tiyata domin ceto rayuwata da rayuwar abun da yake ciki ganin na kasa haihuwar, na katse sosai na yi zaton idan ana shiga da ni ba zan fito da rai ba. Sun fada idan ba ayi haka ba zan iya samun matsala ko abun da ke ciki ya samu, domin haihuwar ce ta zo min babu abun da ya isa ya tare, ma'ana dai zan yi haihuwar bakwaini kamar yadda aka haife ni. Cikin ikon Allah da rahamarsa kamin asuba wani karfin ya zo min, yunkuri daya biyu a uku kan yarinya ya fara fitowa, da na sake yunkurin ta kara fitowa, likitan da ya karbi haihuwata ya yanka gurin ya janyo babyn, azabar sai ta zame min kala biyu, ba ma kamar lokacin da ake dinkewa. Ko ba a fada min na sani yata bata so da rai ba, domin ban ji kukanta a lokacin da ta fado duniya ba. Sai dai ban tabbatar da sai bayan da aka min wanka aka gyara min jikina aka canja tufafina. Sannan Mama ta sake shigowa domin da taimakonta aka yi min komai. Ta shigo dakin da fuska a kumbure da alama ita ma ta yi kuka kamar ni. “Sannu ya karfin jikin na ki?” “Alhamdullahi” Na amsa ina jin maganar ma kamar ba zan iya ba. Domin babu ragowar karfi a jikina kamar ba na da kashi haka nake ji. “Mace kika haifa, amman bata zo da rai ba, na bada ita can gurin dangin mahaifinta, saboda Mahaifiyarki Abdull ta karba” Abu ne da na riga na sani kuma na fahimtar da kaina. Amman da Mama ta fada min sai na ji wani irin babu dadi. Duk wahalar da na sha babyn bata zo da rai ba. Tea mai kauri Mama ta miko min na karba na sha rabin kofin sannan na aje sai ta miko min wayarta. “Kin ganta nan” Na karbi wayar na kalli hoton yarinyar mai kyau da jiki kamar ba yar wata bakwai ba, fara kyakkyawa kamar na kirata ta amsa amman babu rai, an lullube ta da zane gwanin sha'awa. “Yi hakuri, Allah ya baki wata mai albarka, ita kuma Allah yasa mai ceto ce, na tsorata da nakudarki kin wahala har hankalina ya tashi” Na share hawaye na mika mata wayarta. “Mama baki ga waya a jakata ba?” “Na gani, kuma na ga kira na amsa sai na ji muryar abokiyar zamanki wai zaki kashe mata aure Wallahi sai ta ga bayanki, da ta ji muryarta ina mayar mata da martani sai ta kashe bata sake cewa komai ba, fada kuka yi?” Ta banbare magani ta miko min na karba na sha. “Aa ba ni wayar na duba abu” Ta bude jakarta ta dauko wayar ta miko min, sannan ta dauko ragowar tea da na aje ta ba ni. “Daure ki shanye Noor kamin anjima sai ki ji jikinki ya sake, wata kila zuwa gobe su sallame ma idan ba wata matsalar ta biyo ba, yau dai sun ce zaki wuni a nan ki samu bachi” Ba tare da na musa ba na karba na shanye na aje cup din sannan na duba wayata ko zan ga sakon Hana amman shiru. “Ina kika bar Hana ya aka yi kika zo a tare da ita ba? Na kira wayarta kashe mijinki kuma na yi ta kira be daga ba, shiyasa na kira kanwarsa da uwargidanmu na fada musu, su suka kira mahaifiyarsa suka fada mata, kanensa ma jiya duk suna nan mahaifiyarsa kuma a nan ta kwana, ita ta tafi da jaririyar ma, shi din ne dai be kira ba” Wata zuciyar tace na yi mata karyar cewar Hana tana makaranta shiyasa ban zo tare da ita ba. Sai dai tunawa da shawarar da Kareem ya ba ni ya saka na yanke shawarar fada mata gaskiya. “Daman kin ji alamar haihuwar ne kika dawo? Ai kara da kika yi haka a can babu kida kowa sai Hana ita kuma yarinya ce ba sani komai kuka yi ba, ko da yake likitoci ne suke yin komai, amman dai hankali ba zai kwanta ba kara da kika haihu a gida” Na daga kai a hankali na kalli fuskarta, wani tea take kokarin hada min. “Mama” “Na'am” Ta kalleni. “Hana bata tare da ni” Ta kalleni da sauri. “Kamar ya?” “Wani abu ne ya faru, shiyasa na dawo gida ba haihuwa na dawo ba, kuma na dawo ne da takardar saki, Abdull ya sake ni” Ta dauke hannayenta daga tea da take hadawa na biyu tana kallona. “Ya sake ki? Me ya faru? Me kika masa?” “Ban masa komai ba...” Bata bari na karasa ba ta fara min fada. “Karya ne, ba zai sake ki ki dawo gida da ciki wata bakwai haka kawai domin jindadi ba, akwai abun da kika yi?” Na kalleta idanuwana na cika da kwalla. “Me yasa kullum ni ce mai laifi Mama?” “Saboda baki jin magana, ba ki tunani kamin ki aikata abu, gaba daya ke ba rayuwar aure ce a gabanki ba, shiririta kawai kika saka a gaba, wacan auren na farko ma be dade ba ya sake ki, yanzu kuma wannan da ciki ki dawo ki haihu ina murna ki ce min wai ya sake ki? Kin san farincikin da uwa take ji idan ta aurar da yarta Noor? Zaman aure nake son ki ji ba jeka ka dawo ba, yanzu mutane za su fara magana, ba ki gudun abun fada, daman an raya cewar ba zaman aure zaki yi ba, ke dai kin ki zaman aure Noor kin ki zauna” Ta karasa tana kuka, ni ma kukan nake marar sauti. “Ni ma ina da buri, ina da mafarkai irin na kowace mace, sai dai kuma kaddara ta shata min liyi, yadda alƙalamin ya zana dole haka zan bi...” Na lumshe idanuwa. “Daga lokacin da na fahimci haka, sai tsoro da fargabar me zai faru a gaba ya fice a zuciyarta. Tafiyar da babu dawowa ta zama dakuna a yanzu, gashi har kaddarata ta shafi yar'uwata” A take ta daina kukan da take. “Me ya faru me ya samu Hana?” “Abdull ya keta mutuncinta, har ciki ya shiga....” Faduwa Mama ta yi kasa zaune a lokacin da na labarta mata abun da ya faru, ba kuka take ba tagumi ta yi tana kallon kasa. “Yanzu tana ina?” “Ban sani ba” Ya cije baki ta rumtse ido sosai tana girgiza kai. Tashi ta yi ta fice daga dakin ban sake ganin kowa ba sai misalin bakwai wata nurse ta shigo ta yi min allura ta ba ni magani na sha, sannan ta ce anjima likita zai zo ya duba ni, wata kila a sallame ni yau. Haka kuwa aka yi likitan ya zo ya duba na fada masa bana jin komai a yanzu sai rashin karfi sai kuma gurin da aka min dinki ne kawai ke zafi. Magani ya rubuta da allurai masu yawa sannan ya bani takardar sallama misalin karfe biyu na rana. A lokacin Gwaggo Saude da Anty Larai suna asibitin sai kuma kanen Mama biyu. Kai tsaye gidan Baba aka wuce da ni a can ko da muka je mun samu Umma ta dora ruwan zafi, babu bata lokaci ta zuba min a zuba na shiga bandaki na xauna a cikin ruwan da ta zuba shirina na zauna, ga azabar dinki ga na zuwan dake taba gurin ga kuma na zuciya da tunanin yar'uwata. Kowa tambayar yake ina Hana take, sai karya na yi nace jarabawa suke shiyasa ba zai yiyu ta zo ba, kuma na fada musu a hostel take zama ba a gidan ba gudun zargi. Makota suka fara shigowa suna duba ni tare da addu'ar Allah ya ba ni wani mai albarka. Bakinciki be kara min yawa ba sai da dare yayi na gwada number Hana har lokacin a rufe ga kuma bakinciki na haihu amman abun da na haifa babu rai. Kofin ruwan zafin dake hannuna na je na lalabo wayar da Kareem ya ba ni na kira Mama. “Mama” “Noor kina lafiya?” “Ba lafiya ba Mama, na san ke ma kina cikin damuwa” “Ina ciki Noor Kaddara ta riga fata, ni daman ban so tafiyarta, kawai saboda kun matsa ne ke da shi, kuma da san hakan zai kasance da ban bari an yi auren nan ba, ina masa kallon mutumen kirki ne mai sanin ya kamata, jindadi nake hango miki shiyasa na goya masa aka yi auren ina farinciki” Hawaye na zubo ido. “Hana ta kira ki?” “Aa, tashin hankalin kenan, ban san wane hali take ciki ba” “Kareem yace min zai iya kokarinsa ta dawo, amman har yanzu shiru” “Alhaji ma yace zai yi iya kokarinsa za a samota” “Kin fada masa ne?” “Na fada masa cewar daga tafiya makaranta ta bata, ban fada masa abun da dansa ya aikata ba, idan maganar nan ta fita Noor Hana ba zata taba aure ba, babu wanda zai aureta abun yayi muni, fyade kuma har ta yi ciki? Babu wanda zai karbi wannan kadarar, kuma zata kunyata a unguwa zata zama abar kwatance” “Shiyasa ni ma ban fadawa Baba ba, na masa karyar cewar tana hostel din makaranta, saboda bana son Umma ta ji ta yada, amman kuma Mama haka zamu bar Abdull ya tafi a free?” “To ya zamu yi? Sai hakuri, ni dai Allah ya kawo min Yata” “Ameen” Kiran Mama na fita wayata kiran Hana ya shigo, jiki na rawa na daga. “Hana” “Noor” Na daga sai na ji muryar Kareem, fashewa na yi da kuka. “Dan Allah karka ce wani abu ya same ta, dan Allah karka ce ta mutu ka, na haihuwa yata bata zo da rai ba, i lost my baby, bana son sake jin bad news, ya isa haka yanzu” Ina maganar ina kuka sosai sai ya kashe wayar hakan ya tashi hankalina sosai, domin na fahimce ba ya tafe da labari mai dadi, idan ba haka ba me ya kai wayar Hana hannunsa? Me yasa ita ba zata min magana ba? Na dafe zuciyata ina numfashi daker. “Ke Lafiya me ya faru?” Na kasa magana sai kuka nake... KAREEM POV. Yayi ending call din ya nufi wani motarsa ya dafa kamar wanda ya rasa abun yi. Kamin ya dago ya kalli gate din da aka bude motar Safeena ta doso harabar gidan, yana tsaye yana kallonta har ta karaso ta faka motar ta fito sanye da atamfa sai mayafin da be gama rufe jikinta. “I thought i warning you karki sake na yanke duk wata alaka da ke” “Alakata da kai ba zata taba yankewa ba, do you want us to talk about it a nan ko mu shiga ciki?” Ya kalli Mai gadinsa da ya gama rufe gate ya kira shi, ya zo da sauri yana sassarfa. “Ga ni ranka ya dade” “Kalli wannan matar da kyau” Mai gadin ya kalleta da kyau kamar yadda mai gidansa ya ba shi umarni. “Na ganta ranka ya dade” “Daga yau karka bari ta sake shigowa cikin gidan nan, idan ka bari ta sake shigowa a bakin aikinka” “Toh Wallahi ba zata sake ba, ko da kuwa ita din aljanna ce, wuce Hajiya dan Allah ki wuce” Safeena ya rausayar da kai tana kallon Kareem domin ba da wasa ta zo ba. “Really?” Kareem ya daga mishi hannu. “Ban da yau, bar ni zan yi magana da ita” “Toh ranka ya dade” Mai gadin ya juya ya koma, sannan Kareem ya dauke kai ya nufi falon. “Baki da hurumin shigowa gidana, na baki 2 min to talk your rubbish and go” Cewar Kareem bayan ya shigo, sannan ya nufi Center table ya dora wayoyin dake hannunsa ya juyo yana kallonta fuska babu annuri. Safeena ta tabe baki. “Gaskiya ne, hausawa suka ce namiji ba dan goyo ba ne, kuma na gani na tabbatar a yau, har ka manta wacece ni kake fadawa mai gadi kar ya bari na sake shigowa gidanka? Kuma ka ce bana da hurumin shigowa gidan? Saboda me? Ai Yusura bata gidan yanzu, balle ka ce kar ta gani, kuma kana ganin yanke alaka da ni zai sama kama yanci da zaman lafiya ne?” Ya aika mata da wani kallon kaskanci da tsana. “i don't want to see your face, kin cutar da ni iyakar cutarwa, sai yanzu nake hango abun da Momy take guje min, na gode Allah da ban aure ki ba” “Kai ka fara cutar da ni, kai ka fara yaudara da sunan zaka aure ni alhalin kansan mahaifiyarka ba zata bari ba, ina ji ina gani ka aje ni ka auri wata, na yi duk yadda zan iya saboda na cire a zuciya na amman na kasa, bayan na samu mai aurena na yi aure kuma ka sake sabunta min kaunarka har ta kai bana iya gane komai sai naka, na yi sha'awar haihuwa da kai ne saboda ina sonka, amman yanzu na gane na yi babban kuskure domin yaudarata kake a kullum, gashi yanzu na haifi jininka kuma aurena zai lalace bata sigar da nake so ba” Hawaye na mata zuba ta matsa kusa da shi. “All my plan was wata rana zaka aureni, saboda ka saba min da kanka, bana da buri sai na zama da kai, bana jin dadin mu'amala da mijina sai kai, a hakan ka budewa wata zuciyarka ta shiga, kuma ka kwashe sirrina duka ka fada mata, gashi yanzu ta yake ni da shi, igiyar aurena haka ya rage ta katse” Ta muna mishi tazarar dake tsakanin babban yatsanta da mai binsa a yayin da ta kusa hade su. Ta goge hancinta “Ya dauki yaran duka ya auna jininsu kuma na san ya gani, amman be ce min komai ba ya koma Lagos, the next thing da zai biyo na sani saki ne da tozarci a cikin dangi” Ta share hawayenta. “Kanwarsa ta fada min ya fada musu ya Saki Noor amman be fada musu dalilin rabuwar ba, ta dawo gida ta haifi bakwaini, kuma be zo da rai ba, are you planning all this? It's because you love her more then me?” “I didn't plan this, but yes i love her more then you, i love her so much” “And think zan tsaya ina kallonku ku auri junanku ne, bayan kun gama lalata tawa rayuwar? Taya? Ka ci amanata Kareem” Ya daka mata tsawa. “Babu wanda ya lalata rayuwarki, ke kika lalata rayuwarki da kanki, kuma karki zargi kowa a nan” “Anyway na zo na na gargade ka, kuma na fada maka, idan har Abdull ya sake ni to ni ce zan maye gurbin Yusura, na san kai ma ba zaka so mutuncinka ya zube ba, ba zaka so a san ka haihu da matar aure ba, kuma na zo na gargade ka ne, ka fadawa Noor ta fita daga rayuwarka, kuma ta yi taka tsantsan da nata rayuwar domin Wallahi ba zan bar wannan ba” Tsakanin rufe bakinta da kai hannunsa a wuyanta ba za a oya fadar wanda ya riga wani ba, shaketa yayi sosai har sai da idanuwanta suka fito. “You're hurting me Kareem you're hurting me” Baya baya take yana binta. “Karki, taba yarinyar da bata miki komai ba saboda ni, kin cutar da ni that's enough, you have no idea what she's going though, because of your stupid husband, and yanzu kuma ke ki ce zaki saka ta gaba, kuma duk a kaina, ya ishe ki haka” Ta fara bugun hannunsa da karfinta jin da gaske kokarin kasheta yake, she's fighting for her life. Sai da wayarsa ta fara ringing sannan ya sake ta fuska a hade, ita kanta bata taba ganinsa cikin bacin rai irin na yau ba. Tari ta fara tana hakki kamin ta juya da sauri ta fice daga falon. Wayarsa dake ringing ya nufa ya dauka number Yusura ce, for the first time take kiransa bayan rabuwarsu, be haddace number duka ba but ya rike karshen numberta tun a lokacin da take gidan. “Hello” “Sallamu Alaikum” “Wa'alaikumussalam, Lafiya?” “Tine ce bata da lafiya, tun shekaran jiya, an bata magani amman abun be yi ba, jikinta ya tsanani yanzu” “Ganin nan zuwa” Ya sauke wayar ya dauki wayoyin duka biyu ya nufi stairs keys dinsa ya dauko ya sauko ya fita daga falon. 30m ya isa family house dinsu be faka ko'ina ba sai a bangaren da Yusura take tare da kanensa da yaransa. A falo ya same su daga Yusura har Tine din da aka yi ma shimfida a falon. Tun da ya shigo Yusura take kallonsa har ya karaso falon da babu kowa sai yarsa da tsohuwar matarsa dake sanye da katon Hijab domin a yanzu shi din ba muharraminta ba ne. Ya kai hannu ya taba jikin Tine sai ya ji shi da zafi sai dai ba sosai ba, domin bachi ma take. “Me yake damunta?” “Zazzabi ne kawai sai ciwon kai da take cewa ta yawan tari da ciwon ciki” Ya saka hannayensa ya tallafota ya maidata jikinsa yana taba cikin nata, a nan ta bude ido ta kalleshi. “Dady ka zo?” “Eh baki da lafiya” “Eh amman da sauki” “Fada min abun da kike ji” Ta nuna masa gun da ke mata ciwo ta fada masa. “Okay zan siyo miki magani yanzu, idan baki ji sauki ba daga nan zuwa gobe sai mu auna ki mu gani kin ji?” Ta daga mishi kai tana kwantar da kanta jikinsa. “Dady i miss you i miss our home, yaushe zamu koma?” Ya kama hannunta ya rike yana wasa da shi. “Tine akwai abun da ya kamata ku sani, the thing is...” “Yara ne ba za su fahimta ba” Yusura ta tari numfashinsa sai ya daka mata tsawa. “We have to make them understand...” “Are you Okay?” “I'm Not...” Nan ma ya amsa mata a tsawace, Tine ta dago daga jikinsa ta kalleshi “Dady why are you shouting?” “Am... Uhm..” Ya rasa me zai ce, sai ya maida ita kirjinsa ya rumgume. Kamin ya kwantar da ita ya mike tsaye ya fice daga falon. **** **** **** Ta faka a harabar gidanta misalin karfe goma daidai na dare. Kanta ta jinginar a kujerar dake bayanta tana kuka. “So cuta ne Allah ka cire min son bawan Allah nan, shi baya ganina ba ni ce a gabansa ba, ina kaunarsa amman baya gani” Ta fada tana kuka sosai, ta bugi gambun motar. “Ba zan kyale mutanen ba, taya za su lalata rayuwata su kuma su zauna a free? Ni na rayuwa a bakinciki shi kuma ya auri wacce yake so ya rayuwa cikin farinciki? Na san duk shi ya shirya wannan ai daman yana cire ciki, ta kashe aurenta ta fito yanzu ya aureta ko? Tun fa ya rabu da matarsa, bayan ni tawa rayuwar ta gama lalacewa, shiyasa ya fada mata sirrina, to ba ni kadai zai shafa ba har da kai Kareem, ganin yake idan yayi haka zai wanke kansa zai tsira ko? Okay zamu ga ni ai” Ta bude motar ta fita sannan ta share hawayenta ta nufi cikin gidan cikin zafin zuciya tana taba wuyanta da dayan hannunta, dayan kuma yana rike da key din mota.Na dauki awa hudu ina nakudar da ban san da zuwanta sai da muka tafi asibiti, na wahala iya wahala har na yi zaton rai zai yi bankwana da duniya ne. Suka can na yi nishi na yunkura ina ta kokarina, amman kamar bana yi, ban yi zaton haka haihuwa take da da wahala da ciwon fa azaba ba sai da na kai matakin. A lokacin da likitoci suka bada shawarar a shiga ni tiyata domin ceto rayuwata da rayuwar abun da yake ciki ganin na kasa haihuwar, na katse sosai na yi zaton idan ana shiga da ni ba zan fito da rai ba. Sun fada idan ba ayi haka ba zan iya samun matsala ko abun da ke ciki ya samu, domin haihuwar ce ta zo min babu abun da ya isa ya tare, ma'ana dai zan yi haihuwar bakwaini kamar yadda aka haife ni. Cikin ikon Allah da rahamarsa kamin asuba wani karfin ya zo min, yunkuri daya biyu a uku kan yarinya ya fara fitowa, da na sake yunkurin ta kara fitowa, likitan da ya karbi haihuwata ya yanka gurin ya janyo babyn, azabar sai ta zame min kala biyu, ba ma kamar lokacin da ake dinkewa. Ko ba a fada min na sani yata bata so da rai ba, domin ban ji kukanta a lokacin da ta fado duniya ba. Sai dai ban tabbatar da sai bayan da aka min wanka aka gyara min jikina aka canja tufafina. Sannan Mama ta sake shigowa domin da taimakonta aka yi min komai. Ta shigo dakin da fuska a kumbure da alama ita ma ta yi kuka kamar ni. “Sannu ya karfin jikin na ki?” “Alhamdullahi” Na amsa ina jin maganar ma kamar ba zan iya ba. Domin babu ragowar karfi a jikina kamar ba na da kashi haka nake ji. “Mace kika haifa, amman bata zo da rai ba, na bada ita can gurin dangin mahaifinta, saboda Mahaifiyarki Abdull ta karba” Abu ne da na riga na sani kuma na fahimtar da kaina. Amman da Mama ta fada min sai na ji wani irin babu dadi. Duk wahalar da na sha babyn bata zo da rai ba. Tea mai kauri Mama ta miko min na karba na sha rabin kofin sannan na aje sai ta miko min wayarta. “Kin ganta nan” Na karbi wayar na kalli hoton yarinyar mai kyau da jiki kamar ba yar wata bakwai ba, fara kyakkyawa kamar na kirata ta amsa amman babu rai, an lullube ta da zane gwanin sha'awa. “Yi hakuri, Allah ya baki wata mai albarka, ita kuma Allah yasa mai ceto ce, na tsorata da nakudarki kin wahala har hankalina ya tashi” Na share hawaye na mika mata wayarta. “Mama baki ga waya a jakata ba?” “Na gani, kuma na ga kira na amsa sai na ji muryar abokiyar zamanki wai zaki kashe mata aure Wallahi sai ta ga bayanki, da ta ji muryarta ina mayar mata da martani sai ta kashe bata sake cewa komai ba, fada kuka yi?” Ta banbare magani ta miko min na karba na sha. “Aa ba ni wayar na duba abu” Ta bude jakarta ta dauko wayar ta miko min, sannan ta dauko ragowar tea da na aje ta ba ni. “Daure ki shanye Noor kamin anjima sai ki ji jikinki ya sake, wata kila zuwa gobe su sallame ma idan ba wata matsalar ta biyo ba, yau dai sun ce zaki wuni a nan ki samu bachi” Ba tare da na musa ba na karba na shanye na aje cup din sannan na duba wayata ko zan ga sakon Hana amman shiru. “Ina kika bar Hana ya aka yi kika zo a tare da ita ba? Na kira wayarta kashe mijinki kuma na yi ta kira be daga ba, shiyasa na kira kanwarsa da uwargidanmu na fada musu, su suka kira mahaifiyarsa suka fada mata, kanensa ma jiya duk suna nan mahaifiyarsa kuma a nan ta kwana, ita ta tafi da jaririyar ma, shi din ne dai be kira ba” Wata zuciyar tace na yi mata karyar cewar Hana tana makaranta shiyasa ban zo tare da ita ba. Sai dai tunawa da shawarar da Kareem ya ba ni ya saka na yanke shawarar fada mata gaskiya. “Daman kin ji alamar haihuwar ne kika dawo? Ai kara da kika yi haka a can babu kida kowa sai Hana ita kuma yarinya ce ba sani komai kuka yi ba, ko da yake likitoci ne suke yin komai, amman dai hankali ba zai kwanta ba kara da kika haihu a gida” Na daga kai a hankali na kalli fuskarta, wani tea take kokarin hada min. “Mama” “Na'am” Ta kalleni. “Hana bata tare da ni” Ta kalleni da sauri. “Kamar ya?” “Wani abu ne ya faru, shiyasa na dawo gida ba haihuwa na dawo ba, kuma na dawo ne da takardar saki, Abdull ya sake ni” Ta dauke hannayenta daga tea da take hadawa na biyu tana kallona. “Ya sake ki? Me ya faru? Me kika masa?” “Ban masa komai ba...” Bata bari na karasa ba ta fara min fada. “Karya ne, ba zai sake ki ki dawo gida da ciki wata bakwai haka kawai domin jindadi ba, akwai abun da kika yi?” Na kalleta idanuwana na cika da kwalla. “Me yasa kullum ni ce mai laifi Mama?” “Saboda baki jin magana, ba ki tunani kamin ki aikata abu, gaba daya ke ba rayuwar aure ce a gabanki ba, shiririta kawai kika saka a gaba, wacan auren na farko ma be dade ba ya sake ki, yanzu kuma wannan da ciki ki dawo ki haihu ina murna ki ce min wai ya sake ki? Kin san farincikin da uwa take ji idan ta aurar da yarta Noor? Zaman aure nake son ki ji ba jeka ka dawo ba, yanzu mutane za su fara magana, ba ki gudun abun fada, daman an raya cewar ba zaman aure zaki yi ba, ke dai kin ki zaman aure Noor kin ki zauna” Ta karasa tana kuka, ni ma kukan nake marar sauti. “Ni ma ina da buri, ina da mafarkai irin na kowace mace, sai dai kuma kaddara ta shata min liyi, yadda alƙalamin ya zana dole haka zan bi...” Na lumshe idanuwa. “Daga lokacin da na fahimci haka, sai tsoro da fargabar me zai faru a gaba ya fice a zuciyarta. Tafiyar da babu dawowa ta zama dakuna a yanzu, gashi har kaddarata ta shafi yar'uwata” A take ta daina kukan da take. “Me ya faru me ya samu Hana?” “Abdull ya keta mutuncinta, har ciki ya shiga....” Faduwa Mama ta yi kasa zaune a lokacin da na labarta mata abun da ya faru, ba kuka take ba tagumi ta yi tana kallon kasa. “Yanzu tana ina?” “Ban sani ba” Ya cije baki ta rumtse ido sosai tana girgiza kai. Tashi ta yi ta fice daga dakin ban sake ganin kowa ba sai misalin bakwai wata nurse ta shigo ta yi min allura ta ba ni magani na sha, sannan ta ce anjima likita zai zo ya duba ni, wata kila a sallame ni yau. Haka kuwa aka yi likitan ya zo ya duba na fada masa bana jin komai a yanzu sai rashin karfi sai kuma gurin da aka min dinki ne kawai ke zafi. Magani ya rubuta da allurai masu yawa sannan ya bani takardar sallama misalin karfe biyu na rana. A lokacin Gwaggo Saude da Anty Larai suna asibitin sai kuma kanen Mama biyu. Kai tsaye gidan Baba aka wuce da ni a can ko da muka je mun samu Umma ta dora ruwan zafi, babu bata lokaci ta zuba min a zuba na shiga bandaki na xauna a cikin ruwan da ta zuba shirina na zauna, ga azabar dinki ga na zuwan dake taba gurin ga kuma na zuciya da tunanin yar'uwata. Kowa tambayar yake ina Hana take, sai karya na yi nace jarabawa suke shiyasa ba zai yiyu ta zo ba, kuma na fada musu a hostel take zama ba a gidan ba gudun zargi. Makota suka fara shigowa suna duba ni tare da addu'ar Allah ya ba ni wani mai albarka. Bakinciki be kara min yawa ba sai da dare yayi na gwada number Hana har lokacin a rufe ga kuma bakinciki na haihu amman abun da na haifa babu rai. Kofin ruwan zafin dake hannuna na je na lalabo wayar da Kareem ya ba ni na kira Mama. “Mama” “Noor kina lafiya?” “Ba lafiya ba Mama, na san ke ma kina cikin damuwa” “Ina ciki Noor Kaddara ta riga fata, ni daman ban so tafiyarta, kawai saboda kun matsa ne ke da shi, kuma da san hakan zai kasance da ban bari an yi auren nan ba, ina masa kallon mutumen kirki ne mai sanin ya kamata, jindadi nake hango miki shiyasa na goya masa aka yi auren ina farinciki” Hawaye na zubo ido. “Hana ta kira ki?” “Aa, tashin hankalin kenan, ban san wane hali take ciki ba” “Kareem yace min zai iya kokarinsa ta dawo, amman har yanzu shiru” “Alhaji ma yace zai yi iya kokarinsa za a samota” “Kin fada masa ne?” “Na fada masa cewar daga tafiya makaranta ta bata, ban fada masa abun da dansa ya aikata ba, idan maganar nan ta fita Noor Hana ba zata taba aure ba, babu wanda zai aureta abun yayi muni, fyade kuma har ta yi ciki? Babu wanda zai karbi wannan kadarar, kuma zata kunyata a unguwa zata zama abar kwatance” “Shiyasa ni ma ban fadawa Baba ba, na masa karyar cewar tana hostel din makaranta, saboda bana son Umma ta ji ta yada, amman kuma Mama haka zamu bar Abdull ya tafi a free?” “To ya zamu yi? Sai hakuri, ni dai Allah ya kawo min Yata” “Ameen” Kiran Mama na fita wayata kiran Hana ya shigo, jiki na rawa na daga. “Hana” “Noor” Na daga sai na ji muryar Kareem, fashewa na yi da kuka. “Dan Allah karka ce wani abu ya same ta, dan Allah karka ce ta mutu ka, na haihuwa yata bata zo da rai ba, i lost my baby, bana son sake jin bad news, ya isa haka yanzu” Ina maganar ina kuka sosai sai ya kashe wayar hakan ya tashi hankalina sosai, domin na fahimce ba ya tafe da labari mai dadi, idan ba haka ba me ya kai wayar Hana hannunsa? Me yasa ita ba zata min magana ba? Na dafe zuciyata ina numfashi daker. “Ke Lafiya me ya faru?” Na kasa magana sai kuka nake... KAREEM POV. Yayi ending call din ya nufi wani motarsa ya dafa kamar wanda ya rasa abun yi. Kamin ya dago ya kalli gate din da aka bude motar Safeena ta doso harabar gidan, yana tsaye yana kallonta har ta karaso ta faka motar ta fito sanye da atamfa sai mayafin da be gama rufe jikinta. “I thought i warning you karki sake na yanke duk wata alaka da ke” “Alakata da kai ba zata taba yankewa ba, do you want us to talk about it a nan ko mu shiga ciki?” Ya kalli Mai gadinsa da ya gama rufe gate ya kira shi, ya zo da sauri yana sassarfa. “Ga ni ranka ya dade” “Kalli wannan matar da kyau” Mai gadin ya kalleta da kyau kamar yadda mai gidansa ya ba shi umarni. “Na ganta ranka ya dade” “Daga yau karka bari ta sake shigowa cikin gidan nan, idan ka bari ta sake shigowa a bakin aikinka” “Toh Wallahi ba zata sake ba, ko da kuwa ita din aljanna ce, wuce Hajiya dan Allah ki wuce” Safeena ya rausayar da kai tana kallon Kareem domin ba da wasa ta zo ba. “Really?” Kareem ya daga mishi hannu. “Ban da yau, bar ni zan yi magana da ita” “Toh ranka ya dade” Mai gadin ya juya ya koma, sannan Kareem ya dauke kai ya nufi falon. “Baki da hurumin shigowa gidana, na baki 2 min to talk your rubbish and go” Cewar Kareem bayan ya shigo, sannan ya nufi Center table ya dora wayoyin dake hannunsa ya juyo yana kallonta fuska babu annuri. Safeena ta tabe baki. “Gaskiya ne, hausawa suka ce namiji ba dan goyo ba ne, kuma na gani na tabbatar a yau, har ka manta wacece ni kake fadawa mai gadi kar ya bari na sake shigowa gidanka? Kuma ka ce bana da hurumin shigowa gidan? Saboda me? Ai Yusura bata gidan yanzu, balle ka ce kar ta gani, kuma kana ganin yanke alaka da ni zai sama kama yanci da zaman lafiya ne?” Ya aika mata da wani kallon kaskanci da tsana. “i don't want to see your face, kin cutar da ni iyakar cutarwa, sai yanzu nake hango abun da Momy take guje min, na gode Allah da ban aure ki ba” “Kai ka fara cutar da ni, kai ka fara yaudara da sunan zaka aure ni alhalin kansan mahaifiyarka ba zata bari ba, ina ji ina gani ka aje ni ka auri wata, na yi duk yadda zan iya saboda na cire a zuciya na amman na kasa, bayan na samu mai aurena na yi aure kuma ka sake sabunta min kaunarka har ta kai bana iya gane komai sai naka, na yi sha'awar haihuwa da kai ne saboda ina sonka, amman yanzu na gane na yi babban kuskure domin yaudarata kake a kullum, gashi yanzu na haifi jininka kuma aurena zai lalace bata sigar da nake so ba” Hawaye na mata zuba ta matsa kusa da shi. “All my plan was wata rana zaka aureni, saboda ka saba min da kanka, bana da buri sai na zama da kai, bana jin dadin mu'amala da mijina sai kai, a hakan ka budewa wata zuciyarka ta shiga, kuma ka kwashe sirrina duka ka fada mata, gashi yanzu ta yake ni da shi, igiyar aurena haka ya rage ta katse” Ta muna mishi tazarar dake tsakanin babban yatsanta da mai binsa a yayin da ta kusa hade su. Ta goge hancinta “Ya dauki yaran duka ya auna jininsu kuma na san ya gani, amman be ce min komai ba ya koma Lagos, the next thing da zai biyo na sani saki ne da tozarci a cikin dangi” Ta share hawayenta. “Kanwarsa ta fada min ya fada musu ya Saki Noor amman be fada musu dalilin rabuwar ba, ta dawo gida ta haifi bakwaini, kuma be zo da rai ba, are you planning all this? It's because you love her more then me?” “I didn't plan this, but yes i love her more then you, i love her so much” “And think zan tsaya ina kallonku ku auri junanku ne, bayan kun gama lalata tawa rayuwar? Taya? Ka ci amanata Kareem” Ya daka mata tsawa. “Babu wanda ya lalata rayuwarki, ke kika lalata rayuwarki da kanki, kuma karki zargi kowa a nan” “Anyway na zo na na gargade ka, kuma na fada maka, idan har Abdull ya sake ni to ni ce zan maye gurbin Yusura, na san kai ma ba zaka so mutuncinka ya zube ba, ba zaka so a san ka haihu da matar aure ba, kuma na zo na gargade ka ne, ka fadawa Noor ta fita daga rayuwarka, kuma ta yi taka tsantsan da nata rayuwar domin Wallahi ba zan bar wannan ba” Tsakanin rufe bakinta da kai hannunsa a wuyanta ba za a oya fadar wanda ya riga wani ba, shaketa yayi sosai har sai da idanuwanta suka fito. “You're hurting me Kareem you're hurting me” Baya baya take yana binta. “Karki, taba yarinyar da bata miki komai ba saboda ni, kin cutar da ni that's enough, you have no idea what she's going though, because of your stupid husband, and yanzu kuma ke ki ce zaki saka ta gaba, kuma duk a kaina, ya ishe ki haka” Ta fara bugun hannunsa da karfinta jin da gaske kokarin kasheta yake, she's fighting for her life. Sai da wayarsa ta fara ringing sannan ya sake ta fuska a hade, ita kanta bata taba ganinsa cikin bacin rai irin na yau ba. Tari ta fara tana hakki kamin ta juya da sauri ta fice daga falon. Wayarsa dake ringing ya nufa ya dauka number Yusura ce, for the first time take kiransa bayan rabuwarsu, be haddace number duka ba but ya rike karshen numberta tun a lokacin da take gidan. “Hello” “Sallamu Alaikum” “Wa'alaikumussalam, Lafiya?” “Tine ce bata da lafiya, tun shekaran jiya, an bata magani amman abun be yi ba, jikinta ya tsanani yanzu” “Ganin nan zuwa” Ya sauke wayar ya dauki wayoyin duka biyu ya nufi stairs keys dinsa ya dauko ya sauko ya fita daga falon. 30m ya isa family house dinsu be faka ko'ina ba sai a bangaren da Yusura take tare da kanensa da yaransa. A falo ya same su daga Yusura har Tine din da aka yi ma shimfida a falon. Tun da ya shigo Yusura take kallonsa har ya karaso falon da babu kowa sai yarsa da tsohuwar matarsa dake sanye da katon Hijab domin a yanzu shi din ba muharraminta ba ne. Ya kai hannu ya taba jikin Tine sai ya ji shi da zafi sai dai ba sosai ba, domin bachi ma take. “Me yake damunta?” “Zazzabi ne kawai sai ciwon kai da take cewa ta yawan tari da ciwon ciki” Ya saka hannayensa ya tallafota ya maidata jikinsa yana taba cikin nata, a nan ta bude ido ta kalleshi. “Dady ka zo?” “Eh baki da lafiya” “Eh amman da sauki” “Fada min abun da kike ji” Ta nuna masa gun da ke mata ciwo ta fada masa. “Okay zan siyo miki magani yanzu, idan baki ji sauki ba daga nan zuwa gobe sai mu auna ki mu gani kin ji?” Ta daga mishi kai tana kwantar da kanta jikinsa. “Dady i miss you i miss our home, yaushe zamu koma?” Ya kama hannunta ya rike yana wasa da shi. “Tine akwai abun da ya kamata ku sani, the thing is...” “Yara ne ba za su fahimta ba” Yusura ta tari numfashinsa sai ya daka mata tsawa. “We have to make them understand...” “Are you Okay?” “I'm Not...” Nan ma ya amsa mata a tsawace, Tine ta dago daga jikinsa ta kalleshi “Dady why are you shouting?” “Am... Uhm..” Ya rasa me zai ce, sai ya maida ita kirjinsa ya rumgume. Kamin ya kwantar da ita ya mike tsaye ya fice daga falon. **** **** **** Ta faka a harabar gidanta misalin karfe goma daidai na dare. Kanta ta jinginar a kujerar dake bayanta tana kuka. “So cuta ne Allah ka cire min son bawan Allah nan, shi baya ganina ba ni ce a gabansa ba, ina kaunarsa amman baya gani” Ta fada tana kuka sosai, ta bugi gambun motar. “Ba zan kyale mutanen ba, taya za su lalata rayuwata su kuma su zauna a free? Ni na rayuwa a bakinciki shi kuma ya auri wacce yake so ya rayuwa cikin farinciki? Na san duk shi ya shirya wannan ai daman yana cire ciki, ta kashe aurenta ta fito yanzu ya aureta ko? Tun fa ya rabu da matarsa, bayan ni tawa rayuwar ta gama lalacewa, shiyasa ya fada mata sirrina, to ba ni kadai zai shafa ba har da kai Kareem, ganin yake idan yayi haka zai wanke kansa zai tsira ko? Okay zamu ga ni ai” Ta bude motar ta fita sannan ta share hawayenta ta nufi cikin gidan cikin zafin zuciya tana taba wuyanta da dayan hannunta, dayan kuma yana rike da key din mota.“Lafiya Hajiya Lafiya?” Ban kula mai gadin ba na dago da guduna na dawo cikin gidan na nufi jakata na bude na kira number wayarta. Na yi sa'a ta shiga kamin ta amsa har wani jiri nake ganin tsabar bugun da zuciyata yake yi. Ringing tayi ta katse bata daga ba, ina sake kira sai na ji wayar a kashe. Faduwa na yi zaune kan kujerar, ban san abun da zan yi ba, ban san ta ina zan fara nemanta ba. Ban san kowa cikin kawayenta ba. Hana bata da kawaye a garin nan sai yan makaranta kuma ban san waye zan fara bincika ba, ni ban ma san ina makarantarsu yake ba. Takardar na dauka na saka a jakata na koma dakin na dauko babban akwatina na zuba iya kayan da nake iya gani na rufe na janyo akwati na fito ina kuka. Bana son na kira Mama na fada mata domin bana son su san abun da yake faruwa da Hana, musamman Baba da ba fahimta zai yi ba. Idan kuma na koma me zan fada musu? Miye silar mutuwar aurena? Kuma ina zan ce na bar Hana. Ban amsa tambaya ko daya da mai gadin date din yake min ba. Na mike hanya na fara tafiya ina hawaye har na isa babban titi na tari okada na fada masa tashar da zan hau motar Kano zai kai ni. Ya charje ni dubu biyu daga unguwar da nake zuwa unguwar da ya kai na hau mota. Na taki sa'a na isar tashar a lokacin da ake neman mutum daya motar Kano ta tashi na mika duka kudin da nake da su na shiga motar na zauna bayan sun karbi information dina. Tafiyar ta min nisa sosai wata kila saboda mota na hau, domin ban tana zuwa ko dawowa a mota ba sai wannan karon, wata kila kuma saboda abubuwan da suka saka ni gaba ne. Dan carjin da ya rage min na siye ruwa da shi su nayi ta sha, har muka isa Kano. Karfe shida muka sauka garin Kano, domin Tafiyar awa tara ne daga Kano to Lagos a babbar mota. Na fito motar aka cire min akwatina na karba na fara ja zuwa gate din tashar. Napep na shiga na fada masa kasuwar da zai ni, wato kasuwar yan waya. “Dan Allah ka dan jira ni sako kawai zai karbo” “Okay amman Karki dade” “Ba zan dade ba” Na bar akwatina a ciki na shiga cikin kasuwar a lokacin da wasu suke ta hada hadar tashi saboda yamma ta yi. Wani shagon na nufa na nuna masa wayar hannuna. “Malam kuna siyen irin wannan wayar?” Ya kalleni irin duban nan na rashin yarda. Sannan ya karbi wayar ya duba waje da ciki. “Wayar waye?” “Tawa ce siyarwa zan yi” “Saboda me zaki siyar?” “Ina cikin matsalane ina bukatar kudi” “Ina receipt da kwalin wayar” “Suna gida” “To kije ki dauko waya a hannuna haka ai ta sata ce” “Wallahi tawa ce, ka duba ciki akwai hotuna na a ciki, kawai ina cikin matsala ne ina bukatar kudi” Na fada hawaye na jika fuskata. Dayan dake gefensa ya taso ya karbi wayar ya duba. “Nawa zaki siyar” “Ni ban san kudinta ba ku siya kawai” “Iphone 14pro max mu baki 305k kin ga ta dan ji jiki” Na zaro ido ashe babbar waya nake riko ban sani ba. A zatona wayar ba zata wuce 50k ba idan ma ta yi tsada. “Ka dai kara, dan Allah matsala ce ta saka zan siyar Wallahi” Sai ya miko min wayar. “Ba zan iya siyenta fiye da haka ba, siyen waya haka ma ai it's risk kawai dan na ga kina cikin damuwa ne zan siya, kin ga ma yanzu tashi zamu yi” “To kawo kudi” Ya cire min layina ya miko min sannan ya kirgo kudin ya miko min ba tare da na kirga ba na karba ina masa godiya. Na fito da sauri na samu mai napep din nan a inda na bar shi ina shiga ciki ya rufe ni da fada wai na bar shi yana ta jira. “Yi hakuri” “Ina zan kaiki?” “Hotel” Na fada kai tsaye domin kudirin da ya saka na siyar da wayar kenan domin babu sauran kudi a hannuna. “Wace hotel” “Ko wace ma wacce dai mutane ba su cika yawan cikawa ba” Ya fara lissafa min sunayen hotel yana tambayar wacce za zai kai ni. Zuciyata kuma taya raya me kamata na tafi can ba, gida ya kamata na tafi, amman idan na tafi gida me zan fada. “Kai ni ko wace ma” “Okay” Na share hawaye ina jin bakinciki a zuciyata, yau ga ni a garin Kano amman ba damar tafiya gidanmu. Ina yar'uwata take a wane hali take yanzu? Me ye makomar cikin dake jikinta? Me yasa ban saurareta ba wata kila da bata gudu ba. Ya sauke ni a gaban wata katafariyar hotel mai girma da haske ko'ina. “Mu shiga ciki ko na sauke ki a nan?” “Nan ma ya isa” Na fito na dauko akwaiti na bude jakata na dauko 3k cikin kudin wayar na mika masa, sai ya karba yana min godiya. Na juya na hotel din sai kuma na ji bana ra'ayin shiga ciki. Dan haka na tari wata Napep din na shiga domin aiwatar da kudirina. A kofar gidan Kareem mai napep din ya sauke ni, na sallame shi na nufi flowers din da suke gefen gidan na daga akwaitina na jefa a ciki sannan na nufi gate din. Na kwankwasa na san by that time yana gida ko hanyar gida, domin muna hanya aka yi sallah Magariba. Mai gadin ya bude ya leko. “Mai gidan yana nan?” Ina magana numfashi daker domin karfina ya gama karewa ga bakina ya bushe, har lokacin kuma ban ji ina sha'awar komai ba duk da kasancewar ina jin yunwa. “Eh yana nan” “Dan Allah ka ce mishi yana da bako a waje dan Allah ya fito abu ne mai muhimmanci” “Wa zan ce masa?” “Kawai ka fadi haka dai” “Tohm” Ya juya ya koma ya rufe gate din. Ni kuma na kai hannuna na dafa ginin ina jin zuciyata kamar zata fashe. Tun a lagos na kudurtawa zuciyata zuwa na fada masa damuwa ba, da na yi nufin na fara sauka hotel ne washe gari na je na same shi a restaurant ko asibitinsa na fada masa, amman burin ceton yar'uwata ya saka na ji kamar idan ta kai gobe zan iya rasa rayuwarta. Na kwashe minti talatin tsaye a gurin sannan ya sake bude gate din. “Yace a shigo da bakon” Na cira kafa na shiga cikin gidan na fara takawa sai na hango shi tsaye a entrance yana kallona har na karaso. Ya kalli daga kasa har zuwa sama. “Noor” Na kalleshi ba tare da na amsa ba. “Minene kuma wannan karon?” “Kareem na san ina damunka ina shiga rayuwarka da yawa, amman dan Allah karka ce min aa na maka alkawari daga wannan ba za sake ba, dan Allah ka taimaka min dan girman Allah” Na kai kasa ina rokonsa sai kallona yake ya kasa cewa komai. Na nufo shi ne saboda ina jin yana karfi na dukiya wata kila har da hanyar da zai taimaka min. “Shigo ciki” Ya juya. “Matarka za....” “Bata nan” Na mike tsaye na bi bayansa na shiga cikin falon sai na zauna a kujera shi ma ya zauna nesa da ni yana kallona. “Me ya faru?” Na bude jakata na dauko takardar sakin zan tashi na kai masa sai ya taso ya karba ya zauna a dayar kujerar dake kusa da tawa. Yana gama karanta takardar ya kalleni “Innalillahi Wa'inna Illaihirraji'un, Saki Noor mi ya faru?” Na ciro dayar takardar da Hana ta aje min na mika masa ina hawaye. Ya karba ya fara karantawa mikewa yayi tsaye ya girgiza kai ya runtse ido, can kuma ya bude idon ya kalleni. “Da gaske?” Na daga mishi kai har sau uku, ya koma ya zauna na dafe kansa. “Ko da yaushe idan ina cikin damuwa, na kan zo gareka saboda ina samun mafita kuma kana taimaka min, dan Allah ka taimaka min ta dawo, bana son Mama ta sani ko Baba domin idan Baba ya ji zai Fadawa Umma ita kuma zata yada a cikin unguwa, Mama kuma idan ta ji wata kila ba zata iya hakuri zata janyo mutuwar aurenta, bana son daya daga ciki ya faru?” “Na ji zan taimaka miki amman dole ne iyayenki su sani Noor, me zaki fada musu a mutuwar aurenki? Kuma yanzu kamin a gano yar'uwarki me zaki fada? And idan ma an ganta amman ba a cikin hali mai kyau ba dole za su ji ba zaki iya boye wannan ba, yanzu idan kin tafi gida me zaki fada?” “Ba gida zan tafi ba Hotel zan zauna, har sai an gane Hana sai mu tafi gida tare, na Fadawa Baba kawai mun yi fada ne ya sake ni” “Noor yanzu kurciyata tana damunki, matsala irin wannan iyaye kadai suke iya tsayawa mutum, dole ne ki fada musu gaskiya, gidan ba zaki iya Fadawa Baba ba, to ki fadawa Mahaifiyarki, kaddara ce babu wanda ya wuce kaddara” “Kaddarar ita ce kullum a biye da ni, aure na biyu kenan ina yi babu dadi, gashi yanzu har na janyo Hana ta gudu ta shiga duniya” Na fada ina kuka. Mikewa yayi tsaye ya haura sama ya bar ni a falon ina ta kuka ni kadai gaba daya ma duniyar ta isheni. Be dade ba ya sauko da waya a kunnensa. “Yeah let me ask her” Ya kalleni. “Ina kika saka ran zata tafi?” “Ni da ita ba mu san kowa a Lagos ba, ban san inda zata tafi ba, bata da kawaye sai yan karantarsu ban san gurin waye zata tafi ba” “Wai bata san kowa a lagos ba” Can kuma na ji ya amsa da “Okay Thank you” Ya zauna sannan ya amsa kiran da ya shigo. “Aaryam na kira baka daga ba” Ya kalli agogo. “Okay, daman wani taimako nake so dan Allah, wata yarinya ce ta gudu a Lagos nale son a nemo ta, na san kana da friends yan Lagos sosai maybe you can help” Ya mike tsaye ya nufi kitchen ya turo kofar, bana jin komai da yake fada har sai da ya gama wayar ya dawo ya zauna. “Ina wayarki dole sai an tura hotonta” “Na siyar na siyar da ita yanzu, suka ba ni 305” “Wayar?” “Eh” “Saboda me?” “Ba ni da kudi ne, kudin sun kare a hawan mota, shi ne na siyar da wayar saboda na yi amfani da kudin, irin wayarka ne” Ya kalli wayar ya kalleni. “15 pro max suka baki 305k?” “Aa taka ta tsufe tawa da shekara daya, tawa 14pro max ce” Na ciro kudin na zube duka a gurin. “Wane barayo ya siye wayar?” “Ba barawo ba ne shago ne” “Saboda kawai sun ga baki san kan waya ba sai su siye a 305k? Dole sai an nemo hotonta da Yanzu ina layinki yake? Dole sai an nemo hotonta da sunan makaranta su” Na yi shiru ina tunanin gurin da zamu hotonta domin ban zan tafi gida babu ita ba. “A dp dinta na whatsapp akwai hotonta kuma sunan makarantar su Victory College Of Health” “Yanzu ina line ki?” Na saka hannu jaka na dauko layi na mika masa, sai ya karba ya haura sama sai gashi ya sauko rike da wata wayar touching amman ba iPhone ba. Ya saka line da na bashi ya dade yana taba wayar ban sa me yake dubawa ba kamin ya miko min wayar. “Saka number ta” Na karba sakon karta kwane ya rubuta a messager wayar. “Dan Allah Hana ki dawo, tafiyarki ta haifar min da matsaloli da yawa, na bar Lagos na dawo Kano, amman na kasa tafiya gidanmu saboda ban san me zan fada musu ba, bana son na fadawa kowa matsalarki, na miki alkawari babu wanda zai ji, dan Allah ki dawo na yafe miki kuma na fahimce a yanzu, Abdull ya sake ni, Hana kuma kin sani ina da ciki zan iya rayuwa zan iya mutuwa, idan baki dawo gida ba, ni ma zan koma ba, zan tafi na bar garin Kano ne, domin rashin izurin da na yi miki ya hana ni sukuni, ina kaunarki yar'uwata dan Allaj ki dawo, na miki alkawarin babu wanda zai ji” Na saka number ya na dago na mika masa wayar ina kallonsa. Kwarjinsa da kirmarsa sun cika min ido, Kareem mutum har da rabin mutum, shi din mai tsayawa ne akan damuwata mai kokarin ganin bayan abun da ya hana ni farinciki. “Na gode...” Na furta ina hawaye. “kwashe kudin ki tafi gida” “Toh” Na kwashe kudin na saka a jaka sai ya miko min wayar. “Indai yar'uwarki tana sonki da gaske zata dawo ko ta kira ki tsakanin yau zuwa gobe, idan kuma bata kira ba, zamu yi amfani da line mu gano inda take, amman dai zata dawo na miki wannan alkawari ki kwantar da hankalinki” Na daga mishi kai sannan ya karbi wayar na mike tsaye da cikina. “Noor Zauna" Na koma na zauna sai ya tashi ya nufi kitchen be dade ba ya fito rike sandwich da lemu ya janyo karamin lebur ya dora min a kai. “Zaki iya cin wannan? Ko wani abun kike so a kawo miki? Jikina na rawa akwai yunwa a tare da ke” Ban tsaya ba shi amsar zan iya ci ko aa ba na dauka na fara ci. “Kar matarka ta dawo ta same mu a nan” “Ba zata dawo ba. Yaushe rabonki da abinci?” “Rabona da abinci tun jiya bana iya cin komai sai ruwa, gaba daya maza ba su da kirki, Zafeer be fahimce ni yanzu yana can yana cewa na ci amanarsa, na auri Hafiz ban jidadi ba, yanzu kuma wannan” Ajiyar zuciya ya sauke ya bata rai sosai yana kallona. “Wannan duk ya fi su zama dan iska, ni mana ban so aurenki da shi ba, kawai babu yadda zaka hana abun da Allah ya tsara faruwarsa ne, taya zai aikata duk wannan kuma ya sake ki? Ga cikin shi a jikinki” “Ni na ce ya sake ni, ba zan iya zama da shi ba, ba zan iya zama da mazinaci ba” Ina maganar ina kuka har na cinye duka sandwich din na shanye lemu na aje kofi, na mike tsaye Kareem be sake cewa komai ba. Ya dauki cups din ya kai kitchen ya kawo min tissue ma karba ina tsaka da goge hannuna ya jefa min tambaya. “Noor ko da ya tuba?” “Eh, ba zan taba iya zama da namiji mai neman mata ba” “Kina da gaskiya, abu mai kyau na mai kyau ne, go ahead and live your life” Na aje masa tissue a gurin na nufi kofar fita. “Noor, kin san bana baki shawarar da zata cutar da ke ko?” Na juyo na kalleshi. “Daga gidan nan ki tafi gurin Mahaifiyarki kuma ki fada mata komai karki boye mata, ba zaki iya handle wannan ke kadai ba, you're too young for this” Ban ji ina iya musa masa ba, saboda haka na amsa masa da kai sannan na juya na fice daga falon. Mai gadin ne ya bude min gate sai na nuna masa akwatina ya dauko ya ba ni na fara ja har na isa babbar titi na tari Napep na hau na fada masa umguwar da zai kai ni. A daidai gate din gidan Mama ya aje ni na ciro kudinsa na bashi ina jin marata na ciwo sosai. Na fita ina jan akwatin na shiga cikin gidan, hankali be tashi ba sai da na shiga falonta, Mama tana cikin jindadi da kwanciyar hankali, rayuwar da bata samu ba a gidan mahaifinmu gashi a nan ta same ta, anya zan iya zuwa mata da wannan tsarabar? Kaddara ta shafi Hana, yanzu kuma ta shafi Mama...!! Na juya na fara tafiya bana son na zama silar mutuwar auren Mama, ta fada min jikinta be dauki mace a baki komai ba, face rigar da zai iya sakawa ko ya cire. “Subhanallahi” Na juyo jiki babu karfi na kalleta da kumburarrin idanuwana, wani tsadadden green lace ne a jikinta har kyalli yake. “Noor...” Ta fada cike da mamakin ganina. “Lafiya me ya same ki? Jini kike zubarwa” Na sauke kaina kasa na kalli kafata zuwa tile din da jini ya bata gurin da na taka na juyo. Kamar jira ake na kalla sai jiri ya kwashe ni a gurin hudu ya rufe idona marata ta hau murdawa da wani irin radadi da ban taba jin irinsa ba, zafin har cikin bayana yake kai min. Bana iya ganin komai sai muryar Mama da nake ji tana rikona tana kiran sunan wata da ban san wacece ba, a gefe daya kuma ina jin wayar da Kareem ya saka min layi ya ba ni tana ringing... KAREEM POV. Sai da ta fice sannan ya nufi tissue da ta aje ya dauka ya kai hancinsa ya shinshina, yayi baya baya ya zauna ya jinke tissue din. “I deserve this, i lost everything, babu wani abun da ya rage” Ya aje tissue din, be yi addu'a ko fatan Noor ta fito ko wani abun ya sameta a aurenta ba. Shiyasa a lokacin da ta yi auren ya ayyana a ran cewar ya rasata, na tattara lamarinta gaba daya ya aje a gafe, not because of baya sonta but because of yana mata fatan samun farinciki da zaman lafiya, duk kuwa da ya san ba lallai ta samu hakan ba. Saboda Safeena da kuma mijinta. But fada mishi cewar ba zata iya mazinaci ba ko da ya tuba it break him into piece, ya san ya rata ta kenan har bada. Bayan ita kuma babu wata, bayan farincikita babu wani, bayan sonta babu wata, bayan burinta babu wani. “That's okay, it alright Kareem...” Ya furta yana encouraging kansa, ya mike tsaye kenan wayarsa ta yi ringing. Daukar wayar yayi ya duba wata bakuwar number ce da be santa. “Hello..” “Wallahi... Wallahi... Wallahi... Idan Noor ta kashe min aure, kuma ta zama silar tonuwar asirina sai na sai na shuka muku biyar bakinciki kai da ita, domin ba laifinta ba ne ita kadai, har da kai kai da ka fada mata sirrina saboda kana sonta, bata isa ta lalata min rayuwa kuma ita tace zata yi rayuwar jindadi ba” “Excuse me” Ya fada jin muryar Safeena da kuma kalamanta cikin kuka da bacin rai. “Yes ,ina tabbatar maka wannan, domin idan bata fada masa wani abu ba babu yadda zai shigo, haka kurum ya kwashi yara da sunan yawo sai da suka dawo suke fada min asibiti ya kai su aka debi jininsu, kuma duk kai ne sila ai Kareem” Ta kashe wayar tana kuka. Faduwa Kareem yayi zaune saman kujera hannuna rike da wayar ya rufe ido ya dafe kansa. “Noorrrr...! Kai...! Meyasa na aikata ma to? Ita lu'u lu'u ce da na tsallake hanin da Allah yayi na aikata? Why from first plate?” Ya rumtse ido sosai yana jin kamar ya hade zuciya ya mutu, ya san abun da zai biyo baya ba zai musu dadi ba.Na dauki awa hudu ina nakudar da ban san da zuwanta sai da muka tafi asibiti, na wahala iya wahala har na yi zaton rai zai yi bankwana da duniya ne. Suka can na yi nishi na yunkura ina ta kokarina, amman kamar bana yi, ban yi zaton haka haihuwa take da da wahala da ciwon fa azaba ba sai da na kai matakin. A lokacin da likitoci suka bada shawarar a shiga ni tiyata domin ceto rayuwata da rayuwar abun da yake ciki ganin na kasa haihuwar, na katse sosai na yi zaton idan ana shiga da ni ba zan fito da rai ba. Sun fada idan ba ayi haka ba zan iya samun matsala ko abun da ke ciki ya samu, domin haihuwar ce ta zo min babu abun da ya isa ya tare, ma'ana dai zan yi haihuwar bakwaini kamar yadda aka haife ni. Cikin ikon Allah da rahamarsa kamin asuba wani karfin ya zo min, yunkuri daya biyu a uku kan yarinya ya fara fitowa, da na sake yunkurin ta kara fitowa, likitan da ya karbi haihuwata ya yanka gurin ya janyo babyn, azabar sai ta zame min kala biyu, ba ma kamar lokacin da ake dinkewa. Ko ba a fada min na sani yata bata so da rai ba, domin ban ji kukanta a lokacin da ta fado duniya ba. Sai dai ban tabbatar da sai bayan da aka min wanka aka gyara min jikina aka canja tufafina. Sannan Mama ta sake shigowa domin da taimakonta aka yi min komai. Ta shigo dakin da fuska a kumbure da alama ita ma ta yi kuka kamar ni. “Sannu ya karfin jikin na ki?” “Alhamdullahi” Na amsa ina jin maganar ma kamar ba zan iya ba. Domin babu ragowar karfi a jikina kamar ba na da kashi haka nake ji. “Mace kika haifa, amman bata zo da rai ba, na bada ita can gurin dangin mahaifinta, saboda Mahaifiyarki Abdull ta karba” Abu ne da na riga na sani kuma na fahimtar da kaina. Amman da Mama ta fada min sai na ji wani irin babu dadi. Duk wahalar da na sha babyn bata zo da rai ba. Tea mai kauri Mama ta miko min na karba na sha rabin kofin sannan na aje sai ta miko min wayarta. “Kin ganta nan” Na karbi wayar na kalli hoton yarinyar mai kyau da jiki kamar ba yar wata bakwai ba, fara kyakkyawa kamar na kirata ta amsa amman babu rai, an lullube ta da zane gwanin sha'awa. “Yi hakuri, Allah ya baki wata mai albarka, ita kuma Allah yasa mai ceto ce, na tsorata da nakudarki kin wahala har hankalina ya tashi” Na share hawaye na mika mata wayarta. “Mama baki ga waya a jakata ba?” “Na gani, kuma na ga kira na amsa sai na ji muryar abokiyar zamanki wai zaki kashe mata aure Wallahi sai ta ga bayanki, da ta ji muryarta ina mayar mata da martani sai ta kashe bata sake cewa komai ba, fada kuka yi?” Ta banbare magani ta miko min na karba na sha. “Aa ba ni wayar na duba abu” Ta bude jakarta ta dauko wayar ta miko min, sannan ta dauko ragowar tea da na aje ta ba ni. “Daure ki shanye Noor kamin anjima sai ki ji jikinki ya sake, wata kila zuwa gobe su sallame ma idan ba wata matsalar ta biyo ba, yau dai sun ce zaki wuni a nan ki samu bachi” Ba tare da na musa ba na karba na shanye na aje cup din sannan na duba wayata ko zan ga sakon Hana amman shiru. “Ina kika bar Hana ya aka yi kika zo a tare da ita ba? Na kira wayarta kashe mijinki kuma na yi ta kira be daga ba, shiyasa na kira kanwarsa da uwargidanmu na fada musu, su suka kira mahaifiyarsa suka fada mata, kanensa ma jiya duk suna nan mahaifiyarsa kuma a nan ta kwana, ita ta tafi da jaririyar ma, shi din ne dai be kira ba” Wata zuciyar tace na yi mata karyar cewar Hana tana makaranta shiyasa ban zo tare da ita ba. Sai dai tunawa da shawarar da Kareem ya ba ni ya saka na yanke shawarar fada mata gaskiya. “Daman kin ji alamar haihuwar ne kika dawo? Ai kara da kika yi haka a can babu kida kowa sai Hana ita kuma yarinya ce ba sani komai kuka yi ba, ko da yake likitoci ne suke yin komai, amman dai hankali ba zai kwanta ba kara da kika haihu a gida” Na daga kai a hankali na kalli fuskarta, wani tea take kokarin hada min. “Mama” “Na'am” Ta kalleni. “Hana bata tare da ni” Ta kalleni da sauri. “Kamar ya?” “Wani abu ne ya faru, shiyasa na dawo gida ba haihuwa na dawo ba, kuma na dawo ne da takardar saki, Abdull ya sake ni” Ta dauke hannayenta daga tea da take hadawa na biyu tana kallona. “Ya sake ki? Me ya faru? Me kika masa?” “Ban masa komai ba...” Bata bari na karasa ba ta fara min fada. “Karya ne, ba zai sake ki ki dawo gida da ciki wata bakwai haka kawai domin jindadi ba, akwai abun da kika yi?” Na kalleta idanuwana na cika da kwalla. “Me yasa kullum ni ce mai laifi Mama?” “Saboda baki jin magana, ba ki tunani kamin ki aikata abu, gaba daya ke ba rayuwar aure ce a gabanki ba, shiririta kawai kika saka a gaba, wacan auren na farko ma be dade ba ya sake ki, yanzu kuma wannan da ciki ki dawo ki haihu ina murna ki ce min wai ya sake ki? Kin san farincikin da uwa take ji idan ta aurar da yarta Noor? Zaman aure nake son ki ji ba jeka ka dawo ba, yanzu mutane za su fara magana, ba ki gudun abun fada, daman an raya cewar ba zaman aure zaki yi ba, ke dai kin ki zaman aure Noor kin ki zauna” Ta karasa tana kuka, ni ma kukan nake marar sauti. “Ni ma ina da buri, ina da mafarkai irin na kowace mace, sai dai kuma kaddara ta shata min liyi, yadda alƙalamin ya zana dole haka zan bi...” Na lumshe idanuwa. “Daga lokacin da na fahimci haka, sai tsoro da fargabar me zai faru a gaba ya fice a zuciyarta. Tafiyar da babu dawowa ta zama dakuna a yanzu, gashi har kaddarata ta shafi yar'uwata” A take ta daina kukan da take. “Me ya faru me ya samu Hana?” “Abdull ya keta mutuncinta, har ciki ya shiga....” Faduwa Mama ta yi kasa zaune a lokacin da na labarta mata abun da ya faru, ba kuka take ba tagumi ta yi tana kallon kasa. “Yanzu tana ina?” “Ban sani ba” Ya cije baki ta rumtse ido sosai tana girgiza kai. Tashi ta yi ta fice daga dakin ban sake ganin kowa ba sai misalin bakwai wata nurse ta shigo ta yi min allura ta ba ni magani na sha, sannan ta ce anjima likita zai zo ya duba ni, wata kila a sallame ni yau. Haka kuwa aka yi likitan ya zo ya duba na fada masa bana jin komai a yanzu sai rashin karfi sai kuma gurin da aka min dinki ne kawai ke zafi. Magani ya rubuta da allurai masu yawa sannan ya bani takardar sallama misalin karfe biyu na rana. A lokacin Gwaggo Saude da Anty Larai suna asibitin sai kuma kanen Mama biyu. Kai tsaye gidan Baba aka wuce da ni a can ko da muka je mun samu Umma ta dora ruwan zafi, babu bata lokaci ta zuba min a zuba na shiga bandaki na xauna a cikin ruwan da ta zuba shirina na zauna, ga azabar dinki ga na zuwan dake taba gurin ga kuma na zuciya da tunanin yar'uwata. Kowa tambayar yake ina Hana take, sai karya na yi nace jarabawa suke shiyasa ba zai yiyu ta zo ba, kuma na fada musu a hostel take zama ba a gidan ba gudun zargi. Makota suka fara shigowa suna duba ni tare da addu'ar Allah ya ba ni wani mai albarka. Bakinciki be kara min yawa ba sai da dare yayi na gwada number Hana har lokacin a rufe ga kuma bakinciki na haihu amman abun da na haifa babu rai. Kofin ruwan zafin dake hannuna na je na lalabo wayar da Kareem ya ba ni na kira Mama. “Mama” “Noor kina lafiya?” “Ba lafiya ba Mama, na san ke ma kina cikin damuwa” “Ina ciki Noor Kaddara ta riga fata, ni daman ban so tafiyarta, kawai saboda kun matsa ne ke da shi, kuma da san hakan zai kasance da ban bari an yi auren nan ba, ina masa kallon mutumen kirki ne mai sanin ya kamata, jindadi nake hango miki shiyasa na goya masa aka yi auren ina farinciki” Hawaye na zubo ido. “Hana ta kira ki?” “Aa, tashin hankalin kenan, ban san wane hali take ciki ba” “Kareem yace min zai iya kokarinsa ta dawo, amman har yanzu shiru” “Alhaji ma yace zai yi iya kokarinsa za a samota” “Kin fada masa ne?” “Na fada masa cewar daga tafiya makaranta ta bata, ban fada masa abun da dansa ya aikata ba, idan maganar nan ta fita Noor Hana ba zata taba aure ba, babu wanda zai aureta abun yayi muni, fyade kuma har ta yi ciki? Babu wanda zai karbi wannan kadarar, kuma zata kunyata a unguwa zata zama abar kwatance” “Shiyasa ni ma ban fadawa Baba ba, na masa karyar cewar tana hostel din makaranta, saboda bana son Umma ta ji ta yada, amman kuma Mama haka zamu bar Abdull ya tafi a free?” “To ya zamu yi? Sai hakuri, ni dai Allah ya kawo min Yata” “Ameen” Kiran Mama na fita wayata kiran Hana ya shigo, jiki na rawa na daga. “Hana” “Noor” Na daga sai na ji muryar Kareem, fashewa na yi da kuka. “Dan Allah karka ce wani abu ya same ta, dan Allah karka ce ta mutu ka, na haihuwa yata bata zo da rai ba, i lost my baby, bana son sake jin bad news, ya isa haka yanzu” Ina maganar ina kuka sosai sai ya kashe wayar hakan ya tashi hankalina sosai, domin na fahimce ba ya tafe da labari mai dadi, idan ba haka ba me ya kai wayar Hana hannunsa? Me yasa ita ba zata min magana ba? Na dafe zuciyata ina numfashi daker. “Ke Lafiya me ya faru?” Na kasa magana sai kuka nake... KAREEM POV. Yayi ending call din ya nufi wani motarsa ya dafa kamar wanda ya rasa abun yi. Kamin ya dago ya kalli gate din da aka bude motar Safeena ta doso harabar gidan, yana tsaye yana kallonta har ta karaso ta faka motar ta fito sanye da atamfa sai mayafin da be gama rufe jikinta. “I thought i warning you karki sake na yanke duk wata alaka da ke” “Alakata da kai ba zata taba yankewa ba, do you want us to talk about it a nan ko mu shiga ciki?” Ya kalli Mai gadinsa da ya gama rufe gate ya kira shi, ya zo da sauri yana sassarfa. “Ga ni ranka ya dade” “Kalli wannan matar da kyau” Mai gadin ya kalleta da kyau kamar yadda mai gidansa ya ba shi umarni. “Na ganta ranka ya dade” “Daga yau karka bari ta sake shigowa cikin gidan nan, idan ka bari ta sake shigowa a bakin aikinka” “Toh Wallahi ba zata sake ba, ko da kuwa ita din aljanna ce, wuce Hajiya dan Allah ki wuce” Safeena ya rausayar da kai tana kallon Kareem domin ba da wasa ta zo ba. “Really?” Kareem ya daga mishi hannu. “Ban da yau, bar ni zan yi magana da ita” “Toh ranka ya dade” Mai gadin ya juya ya koma, sannan Kareem ya dauke kai ya nufi falon. “Baki da hurumin shigowa gidana, na baki 2 min to talk your rubbish and go” Cewar Kareem bayan ya shigo, sannan ya nufi Center table ya dora wayoyin dake hannunsa ya juyo yana kallonta fuska babu annuri. Safeena ta tabe baki. “Gaskiya ne, hausawa suka ce namiji ba dan goyo ba ne, kuma na gani na tabbatar a yau, har ka manta wacece ni kake fadawa mai gadi kar ya bari na sake shigowa gidanka? Kuma ka ce bana da hurumin shigowa gidan? Saboda me? Ai Yusura bata gidan yanzu, balle ka ce kar ta gani, kuma kana ganin yanke alaka da ni zai sama kama yanci da zaman lafiya ne?” Ya aika mata da wani kallon kaskanci da tsana. “i don't want to see your face, kin cutar da ni iyakar cutarwa, sai yanzu nake hango abun da Momy take guje min, na gode Allah da ban aure ki ba” “Kai ka fara cutar da ni, kai ka fara yaudara da sunan zaka aure ni alhalin kansan mahaifiyarka ba zata bari ba, ina ji ina gani ka aje ni ka auri wata, na yi duk yadda zan iya saboda na cire a zuciya na amman na kasa, bayan na samu mai aurena na yi aure kuma ka sake sabunta min kaunarka har ta kai bana iya gane komai sai naka, na yi sha'awar haihuwa da kai ne saboda ina sonka, amman yanzu na gane na yi babban kuskure domin yaudarata kake a kullum, gashi yanzu na haifi jininka kuma aurena zai lalace bata sigar da nake so ba” Hawaye na mata zuba ta matsa kusa da shi. “All my plan was wata rana zaka aureni, saboda ka saba min da kanka, bana da buri sai na zama da kai, bana jin dadin mu'amala da mijina sai kai, a hakan ka budewa wata zuciyarka ta shiga, kuma ka kwashe sirrina duka ka fada mata, gashi yanzu ta yake ni da shi, igiyar aurena haka ya rage ta katse” Ta muna mishi tazarar dake tsakanin babban yatsanta da mai binsa a yayin da ta kusa hade su. Ta goge hancinta “Ya dauki yaran duka ya auna jininsu kuma na san ya gani, amman be ce min komai ba ya koma Lagos, the next thing da zai biyo na sani saki ne da tozarci a cikin dangi” Ta share hawayenta. “Kanwarsa ta fada min ya fada musu ya Saki Noor amman be fada musu dalilin rabuwar ba, ta dawo gida ta haifi bakwaini, kuma be zo da rai ba, are you planning all this? It's because you love her more then me?” “I didn't plan this, but yes i love her more then you, i love her so much” “And think zan tsaya ina kallonku ku auri junanku ne, bayan kun gama lalata tawa rayuwar? Taya? Ka ci amanata Kareem” Ya daka mata tsawa. “Babu wanda ya lalata rayuwarki, ke kika lalata rayuwarki da kanki, kuma karki zargi kowa a nan” “Anyway na zo na na gargade ka, kuma na fada maka, idan har Abdull ya sake ni to ni ce zan maye gurbin Yusura, na san kai ma ba zaka so mutuncinka ya zube ba, ba zaka so a san ka haihu da matar aure ba, kuma na zo na gargade ka ne, ka fadawa Noor ta fita daga rayuwarka, kuma ta yi taka tsantsan da nata rayuwar domin Wallahi ba zan bar wannan ba” Tsakanin rufe bakinta da kai hannunsa a wuyanta ba za a oya fadar wanda ya riga wani ba, shaketa yayi sosai har sai da idanuwanta suka fito. “You're hurting me Kareem you're hurting me” Baya baya take yana binta. “Karki, taba yarinyar da bata miki komai ba saboda ni, kin cutar da ni that's enough, you have no idea what she's going though, because of your stupid husband, and yanzu kuma ke ki ce zaki saka ta gaba, kuma duk a kaina, ya ishe ki haka” Ta fara bugun hannunsa da karfinta jin da gaske kokarin kasheta yake, she's fighting for her life. Sai da wayarsa ta fara ringing sannan ya sake ta fuska a hade, ita kanta bata taba ganinsa cikin bacin rai irin na yau ba. Tari ta fara tana hakki kamin ta juya da sauri ta fice daga falon. Wayarsa dake ringing ya nufa ya dauka number Yusura ce, for the first time take kiransa bayan rabuwarsu, be haddace number duka ba but ya rike karshen numberta tun a lokacin da take gidan. “Hello” “Sallamu Alaikum” “Wa'alaikumussalam, Lafiya?” “Tine ce bata da lafiya, tun shekaran jiya, an bata magani amman abun be yi ba, jikinta ya tsanani yanzu” “Ganin nan zuwa” Ya sauke wayar ya dauki wayoyin duka biyu ya nufi stairs keys dinsa ya dauko ya sauko ya fita daga falon. 30m ya isa family house dinsu be faka ko'ina ba sai a bangaren da Yusura take tare da kanensa da yaransa. A falo ya same su daga Yusura har Tine din da aka yi ma shimfida a falon. Tun da ya shigo Yusura take kallonsa har ya karaso falon da babu kowa sai yarsa da tsohuwar matarsa dake sanye da katon Hijab domin a yanzu shi din ba muharraminta ba ne. Ya kai hannu ya taba jikin Tine sai ya ji shi da zafi sai dai ba sosai ba, domin bachi ma take. “Me yake damunta?” “Zazzabi ne kawai sai ciwon kai da take cewa ta yawan tari da ciwon ciki” Ya saka hannayensa ya tallafota ya maidata jikinsa yana taba cikin nata, a nan ta bude ido ta kalleshi. “Dady ka zo?” “Eh baki da lafiya” “Eh amman da sauki” “Fada min abun da kike ji” Ta nuna masa gun da ke mata ciwo ta fada masa. “Okay zan siyo miki magani yanzu, idan baki ji sauki ba daga nan zuwa gobe sai mu auna ki mu gani kin ji?” Ta daga mishi kai tana kwantar da kanta jikinsa. “Dady i miss you i miss our home, yaushe zamu koma?” Ya kama hannunta ya rike yana wasa da shi. “Tine akwai abun da ya kamata ku sani, the thing is...” “Yara ne ba za su fahimta ba” Yusura ta tari numfashinsa sai ya daka mata tsawa. “We have to make them understand...” “Are you Okay?” “I'm Not...” Nan ma ya amsa mata a tsawace, Tine ta dago daga jikinsa ta kalleshi “Dady why are you shouting?” “Am... Uhm..” Ya rasa me zai ce, sai ya maida ita kirjinsa ya rumgume. Kamin ya kwantar da ita ya mike tsaye ya fice daga falon. **** **** **** Ta faka a harabar gidanta misalin karfe goma daidai na dare. Kanta ta jinginar a kujerar dake bayanta tana kuka. “So cuta ne Allah ka cire min son bawan Allah nan, shi baya ganina ba ni ce a gabansa ba, ina kaunarsa amman baya gani” Ta fada tana kuka sosai, ta bugi gambun motar. “Ba zan kyale mutanen ba, taya za su lalata rayuwata su kuma su zauna a free? Ni na rayuwa a bakinciki shi kuma ya auri wacce yake so ya rayuwa cikin farinciki? Na san duk shi ya shirya wannan ai daman yana cire ciki, ta kashe aurenta ta fito yanzu ya aureta ko? Tun fa ya rabu da matarsa, bayan ni tawa rayuwar ta gama lalacewa, shiyasa ya fada mata sirrina, to ba ni kadai zai shafa ba har da kai Kareem, ganin yake idan yayi haka zai wanke kansa zai tsira ko? Okay zamu ga ni ai” Ta bude motar ta fita sannan ta share hawayenta ta nufi cikin gidan cikin zafin zuciya tana taba wuyanta da dayan hannunta, dayan kuma yana rike da key din mota.Cikin motar ya shiga ya zauna ya lumshe idonta yana maida numfashi a hankali. Be dago ba sai da ya ji ana buga gilashin motar, juyawa yayi a hankali ya duba sai ya ga Areef tsaye rike da ipad. Ya sauke gilashin kasa yana murmushi “Areef my love” “Dady na hango ka ta window Hajiya” Ya bude motar gaba daya ya dauko dansa ya zauna a saman jikinsa ya kwantar da shi jikinsa. “Ka iya gulma ko Areef?” Yayi dariya yana boye fuskarsa, Kareem ma murmushin yayi ya shafa bayan dansa. Yaransa na cikin farinciki da Allah ya ba shi domin yana son yara ko ba nasa ba balle kuma jininsa. Slowly ya sauke ajiyar zuciya tunawa da yayi da Noor ta raya abun da ta haifa, shi da yake namiji yake son yara balle kuma ita da haifa da kanta kuma ta yi nagudar abunta, ya lalabo wayarsa ya sake kiran line Noor da wayar yar'uwarta. Ta amsa kiran tana kuka sai har yana jinta. “What now ta mutu ko?” “I'm sorry for your lost, Allah ya baki wani mai albarka, and your sister...” Yayi shiru for a while sannan ya furta. “She's safe, but tana asibiti saboda ta dan bugu da mota, ba mu san yaushe ba amman haka aka zo mana da ita, amman tana raye” “Ka rantse ka ce wallahi tana raye tana duniya” “Me zai saka na yi miki karya?” “Saboda na jidadi na kwantar da hankalina” Murmushi mai kyau ya fadada fuskarsa. “Kin sa ina son kwanciyar hankalinki kenan?” “Eh na sani fada min gaskiya” “Wallahi tana da rai tana asibiti” “Me yasa ba zata yi magana ba? Me yasa kai kake rike da wayarta?” “Saboda tana bachi, kuma na kira na fara tambayarki ko kin fadawa iyayenki gaskiyar abun da ya faru so that na san ya zan musu bayani” “Na fadawa Mama ba ka ce na fada ba, amman Baba be sani ba, mama tace kar a fada masa tace ace bata ta yi kawai” “Okay zan fada musu yanzu an gano ta” “Zaka kira Mama yanzu?” “Yeah” “Zan aje wayar ka kirata sai na tabbatar da gaske kake tana raye” Yayi murmushi. That's why i love you, ya fada a ransa a zahiri kuma sai ya amsa mata da “Okay” Ta katse kiran sai ya aje wayar ya murza key din motar ya fara tukawa tare da dansa ya tafi ya siyo maganin ya rubuta yadda zata sha sannan yayi mata tsarabar gasasshiyar kaza da snack domin ya san tana sonsu sosai, sannan ya dawo gidan Areef ya rika masa leda daya ya shiga ciki wannan karon ya same ta tana kallon tv ne ta lulluba da bargo. “Tine ya jikin?” “Na ji sauki” Ya aje mata tsarabar ya bude maganin da kansa ya bata sannan yayi mata sallama tare da Areef ya fice, Uffan be cewa Yusura ba dake zaune a gafe daya tana kallonsu. Bangaren Hajiya ya shiga ya gaisa da ita da kannensa sannan ya fito ya nufi asibitin... NOOR POV. Hankali be kwanta ba har sai da kiran Mama ya shigo wayata ta fada min Kareem ya kira da wayar Hana ya fada mata tana asibiti, rumgume wayar na yi ina jin wani irin kima da mutuncin Kareem a ido na, na yarda wani lokacin Allah ya kan kawawa bawa abun da be yi zato ba, ina jin Allah ya hada ni da Kareem ne domin ya share min hawayen abububuwa da yawa. Umma na kwalawa kira domin tun dazun take tambaya me ua faru na gagara fada mata saboda kuka, tana shigowa na fada mata cewar kukan da nake Hana ce ta bata daga sunan tafiya makaranta amman an ganta tana asibiti yanzu haka. Tun daga ranar kusan rabi damuwata sai na ji ya gushe, domin yar'uwata yana raye, rabuwa da miji abu ne mai sauki, kamar yadda samun wani dan ko yar yake da sauki a gurin Allah. Duk yadda na so na tafi ganinta ban samu dama ba, sai waya na yi da ita, shi ma kuma sai washe gari bayan ta farka. Sai da na yi kwana uku sannan Baba ya yarda na tafi na ganta tare da kawata Zainab, da ake ta shirye shiryen aurenta a watan nan. Da dare muka fita saboda gujewa idanuwan mutane, Napep muka hau yana fara tafiya na kira Kareem na fada masa cewar zan zo na duba Hana. “Bana asibitin yanzu, ba ki san gurin ba?” Ban san gurin ba, amman Zainab ta sani domin ta je duba ta kamar yadda mutane unguwa da yawa suka je dubata, but i just neet to see him so nake na masa godiya i just miss him. “Ni ban san gurin ba” “Okay a me kika zo?” “Napep” “Ina family house yanzu nan na shigo, amman zan saka Aaryam ya zo ya tare ki? Ya nuna miki gurin. Kuma ina tunanin akwai wata kanwar mamanku a can ko ki kirata” Na kashe wayar ba tare da nace masa komai ba. Sai dai ga mamaki ina mai napep na sauke mu a bakin asibitin sai hangon shi na yi ya taho da kafa zuwa inda muke tsaye. “Ashe ku biyu kuke?” Ina kallonsa murmushi ya zo min for no reason na sauke kaina kasa kamar mai jin kunya, murmushi ya mayar min ya kalli Zainab. “Kawarmu ce wannan?” “Eh sunanta Zainab” Zainab ta gaishe shi ya amsa, sannan ya juya yana kallon wani mai kama da shi da ya doso inda muke yana fadin. “Ga key dinka ka shiga da motar ka ciki, sai mu taka na nuna mata gurin” Kareem ya ce. “Malam kai zaka ja motar ka shiga da ita ciki” “Aa Wallahi, ai ba motata ba ce kuma ba asibitina ba ce” “Amman kai ka nace sai ka biyo ni” “Da na ji ita ce ba, saboda na ganta mana, malama bismillah ga hanyar nan” Ya nuna min titi da zamu mike da hannunsa, ni kuma na kalli Kareem irin kallon nan na jiran umarni. “Karki damu, ni kanensa ne uwa daya uba daya, muje ke kuma kawarta ku je ya sauke ki inda zai faka motar” Kareem ya karbi keys din hannunsa ya juya ya nufi gurin da motar take fake tare da Zainab. Ni da kanensa kuma muka fara takawa a kafa zuwa cikin asibiti dauriya kawai nake domin ina jin zafin dinkin da aka min har yanzu. “Sunana Aaryam” “Nice” Na fada feeling so nervous. “Ke fa ya sunanki?” “Noor” “Haka ne na tuna, na san baki san ni ba ko?” “Eh” “Haka ne, ni ma ina dan jin sunanki gurin big bro ne can sama haka” Now kuma I'm feeling awkward like Kareem yana hirata ne da mutane? Domin Hafiz ma haka ya taba fada min farkon haduwarmu. “Ni nake bin Kareem, shi ne babba a dakinmu, muna da kanen mata akwai daya da Momy ta bari sai kuma yaran Hajiya su uku, sai kuma Yusura” Na kalleshi kamar na yi maganan sai kuma na fasa. Ashe ya lura “Na san zaki ce Yusura ba matar Kareem ba ce?” Na daga mishi kai. “Haka ne, amman a gidanmu take zama a nan ta girma” Ya ba ni labarin zamanta a gidan yadda aka yi aurenta da Kareem da kuma rashin son junansu da suke. “Amman a haka Kareem yayi kokari ya bata duka hakokinta, har sai da ta nemi saki so yanzu sakin da yayi mata babu gyara a tsakaninsu” Mamaki ya kama ni, Kareem be fada min ya saki matarsa, wata kila shiyasa yake cewa ba zata zo ta tararda da mu ba, jin cewar bata sonsa kuma ba sabu abu ba ne na fahimta tun a zuwana na farko gidan, kamin shi kansa Kareem din ya fada min yadda aka yi auren a wacan ranar da ya fada min sirrinsa. “To yanzu yaran fa?” “Suna hannunta, idan Kareem yana son ganinsu zai zo ya gansu ne sai ya koma, shi kadai yake rayuwa a gidan yanzu, yana cikin kadaici da ban tausayi sosai, gashi ya rasa yarinyar da ya so ya aura, abun ba dadi, ni ba zan iya biyayyar da Kareem yayi ba, ba zan iya auren macen da bana so ba, auren kiyayya ba shi da dadi shiyasa Yayana yake matukar ba ni tausayi, yana da zuciya da hallaya masu kyau, amman har yanzu be samu farinciki ba” Tausayinsa ya kama ni sosai domin na san yadda rayuwa da wanda baka so take, na gwada na san yadda ake ji. “Kin san me yasa nake baki labarin nan?” Na amsa masa da alamar ban sani ba. “I want you to be his best friend, domin yanzu ba shi da abokin shawara ya rasa Hafiz, ya rasa mahaifiya ni kuma tawa safgar nake dabam, na lura da wani abu yayana yana samun farinciki idan kuna tare ko yana zancenki, please idan kin ganshi a cikin damuwa ki yi kokarin cire shi, kuma ki yi iya yadda zaki iya ki ga ya auri wacce yake so take ba shi farinciki yana cikin damuwa sosai...” Aaryam yana maganar ina kallon Kareem dake tsaye hannayensa zube a aljihu yana jiran karasowarmu. “Kin min alkawari zaki saka shi ya auri wacce yake so? Shi ma ya samu farinciki kamar kowa? Farincikinsa shi ne na mu, and don't tell anyone mun yi maganar nan” Ban iya amsa masa da eh ko aa ba har muka isa gurin da Kareem yake shi kadai yana kallonmu. Da dan zargi yake kallon kanensa sai Aaryam ya daga masa hannu ba tare da ya ce komai ba ya wuce cikin asibiti. Sai da na daina hango shi sannan na juyo na kalli Kareem. “Me ya fada miki?” “Yadda akan samu Hana” Na amsa kai tsaye. “Come on karki wasa da ni mana, na san ki fa” Na yi murmushi. “Ba ka ce ba zaka zo ba?” “Na ji kamar hakan da na fada be miki dadi ba, shiyasa kika yanke wayar maybe you want to see me huh?” Ya daga min gira sai na yi murmushi “I miss you, i just wanna say thank you, ban taba haduwa da wani mutum mai karamci da sanin ya kamata da kawaici da son farinciki ba sai Kareem, ba alakar uwa ba ta uba amman komai nake so kana yi min, people like you a rare, kai mutumen kirki ne, kai mutum ne mai damuwa da damuwar wani, Allah ya faranta maka ya baka abun da kake nema Kareem” Yayi murmushi mai kyau ya daga kansa yana kallon saman kaina domin yana tsaye ne a matakar dake bawa mutum damar hawa ward din dake cike da mutane, ni kuma ina kasa daman ya fi ni tsayi balle ya hau akan abu. “Kalamanki sun lashi zuciyata, a duk lokacin da kike bukatar wani abu, ko wani ya taba ki just come to me zan miki duk abin da kike so, if you ever need safe just come to me” “Da me zan saka maka Kareem?” Yayi dariya mai dadin sauraro. “Thank you, just let me be right beside you in anything you do” Ya fada yana lumshe ido. Na yi murmushi ina kallon mutane fake ta kai da kawo. “Mu je ciki ki ganta” Muka jera muna tafiya sai kamshi yake mai kwantar da hankali. “Kareem” “Uhm mmn” “Ina Yusura?” Ya tsaya cak ya daina tafiyar da yake ya kalleni. Zai yi magana wani mutum ya ba shi hannu suka gaisa, after ya gaisa da shi ya juyo ya kalleni. “Ina wannan ya fito kuma?” “Kawai ka amsa min mana” “Tana gida family house dinmu, ba ma tare yanzu” “I'm happy for both of you, rayuwa da wanda baka so ba shi da dadi” Ya sauke gutun numfashi. “Haka ne, rayuwa mutum shi kadai ma bata da dadi, amman dai da sannu zan saba” “Ai ba haka zaka zauna ba, zaka yi aure kai ma ka auri wanda kake so take sonka” “Ba zan taba wani auren ba Noor, yarinya daya nake so kuma na rasa ta, shi ke nan, ba zan sake son wata ba” “Maybe zaka iya son wata, ita ma ai baka san zaka sota ba sai daga baya ko?” “No tun farko haduwa da wannan yarinyar na ji wani akanta, amman ban fahimta sai daga baya, kuma yanzu na yi latti I'm not the one she mean to find, every thing keep us apart, amman ni na san ina kaunarta sosai, i love her so much” Ban san miyasa ba, na dan ji babu dadi da yace yana kaunarta sosai. “Amman ka yi sanyi ne da baka same ta ba? Kai din nan babu wanda zata ce bata sonka” “Na je ne a makare, wani ya riga ni shiga zuciyarta, kuma ita dai tana jin ban mata ba zata iya aurena ba, har yanzu bata da wayo bata gama fahimtar duniya ba, amman dai zan jira har lokacin da zata yi hankali ta natsu ta fahimce ni, maybe we can rewrite the start...” Na masa duba mai cike da tambayoyi, na ji wani bangare na zuciyata na raya min ko dai da ni yake.? “Ya sunanta ma?” “Sunanta Hafsat” “Ta yi aure ai ka ce ko?” “Eh” “To tace maka zata fito ne da ka ce zaka jira ta?” “No, tana gidan mijinta har yanzu” Ya bude min kofar dakin yana kallon cikin idanuwa. “Noor” Kiran da Hana ta yi min ya saka na dauke idona daga kallon Kareem na kalleta, na shiga dakin da farinciki da murna da jindadi sosai ta ji rauni a kai da kai da kuma hannu har an saka mata bandeje an daure. Na rumgume sai ta fashe da kuka sosai. “Inna a ba su guri su tattauna mana, Aaryam mu tafi ko?” Ina jin lokacin da Kareem yake fadar haka, ban dago ba sai da suka fice gaba daya daga dakin har kanwar Mama. “Dan Allah ki yi hakuri, da na sani ba zan je na zauna a gidanki ba Wallahi” “Ba laifinki ba ne, halinsa ne daman da ace ba halinsa ba ne ba zai fara ba, ke ya kamata na bawa hakuri na janyo ki a jiki gashi sanadina kin cutu, kuma ban fahimce ki ba sai da kika tafi” “Haka Allah ya tsara min, ban isa na wuce wannan ba, arziki na ma daya an cire cikin” Na dafata. “An cire? Waya cire? Yaushe?” “Tun a ranar da na dawo yayi min allurar amman sai jiya ya dauke ni ya kai ni wani gida wata nurse ta wanke min marata yace an cire komai?” Farinciki ya lullube ni. “Amman ta sani amman?” “Eh ta sani, tare muka je da ita yace a bar maganar ne ba sai an fadawa kowa ba, kanensa ma be sani ba” Na sake rumgume ta ina jin kamar Kareem na rumgume tsabar farinciki. “Amman Kareem din nan son ki yake yi ko Noor?” Na dago daga jikinta “Aa be taba nuna min ba, be taba fada min ba” “Kyautatawar da yake miki ta wuce misali” “Wata kila saboda ina matar abokinsa ne, kuma yana da tausayi ke ma kin ba shi tausayi shiyasa ya saka aka cire cikin” Na sauke kanta kasa hawaye suka sake idonta. “Na yi nufin kashe kaina, lokacin da na bar gidanki, ba ni da gurin tafiya, kuma ba zan iya koma gida ba, da kaina na tara kaina a titi mota ta bugu ni, amman ban mutu ba sai na ji ciwo a hannu da kafa da kai, mutumen be tsaya kai ni asibiti ba ya gudu, sai mutane ne suka taimaka min suka kai ni, su ma suna kai ni suka gudu, asibitin kuma suka ce ba za su taba ni ba, sai da dansa kuma sai an siye kati, a gurin aka bar ni wulakance, sai da wahala ta yi min yawa na kunna wayar na ga sakonki, da kuma wani sakon ta wata number yace min shi Aaryam ne idan ina bukatar taimako na fada masa, a madadin na kira ki sai na kira shi, da muka yi magana sai yace kar na kira ki, shi yasa aka dauko ni daga can aka kawo ni Kano. Abdull ba zai gama lafiya ba, kuma na jidadi da baki samu ďa da shi ba Noor, ni kadai na san me nake ji a raina, kuma shi kenan ya sha a free babu abun da za a masa” “Saboda gudun abun da zai biyo ba ne, Mama ta ce idan wani ya ji ba za a aure ki ba, kuma zai zama abun magana a cikin unguwarmu, amman ki kaiwa Allah kararsa zai saka miki” “Kullum sai na fadawa Allah, ina masa Allaj ya isa, amman wannan abun ba zai taba gogewa ba” Turo kofar dakin da aka yi ne ya saka ta yi saurin share hawayenta ni ma na share nawa. Zainab ce take fadar na tashi mu tafi dare yayi, Mama Talatu ma ta dawo dakin sai na yi mata sallama sannan muka tafi. A napep ma Zainab ta tambaye ni kwatankwacen abun da Hana ta tambaye ni cewa wai Kareem so na yake. “Be taba fada min ba” “Amman ke baki lura ba, ji yadda yake kallonki fa, kuma yana ta yi min tambayoyi a kanki” “Amman ni be taba cewa yana so na ba, kuma yana ma da wacce yake so sunanta Hafsatu” “Ikon Allah, toh amman dai abun da mamaki wata kila jini ne ya hadu ko kuma ya riga ya fara sonta ne ba yadda zai yi da ke” “Tun kamin ya hadu da ita fa, muke tare ai da ya fada min, kuma ni bana ma son shi” Na yamutsa fuska tunawa da na yi da wani abu. Zainab ta gwalo ido. “Saboda me?” “Haka nan dai” “Tab Wallahi baki san abun da kike so ba, kamar wannan zaki ce baki son shi? Mutum mai kyau mai kudi mai komai, ko ni za'ayi aurena a watan nan Wallahi yace yana so na zan iya balle auren na aure shi” Na kalleta da mamaki sai kuma na ji haushinta na fadar hakan fa ta yi ban sake cewa komai ba har muka sauka Napep din. Komai ya zamar mana kamar labari, ni na danne ciwon zuciyata Hana ma ta danne nata mun barwa Allah komai muka koma cigaba da rayuwa kamar yadda muka saba, a bayan. Sai wani shakuwa da kaunarnan junanmu da tausayi ya kara shigarmu, Mama kuma tana ta rayuwa a gidan aurenta ba tare da wani tashin hankali ba. Abun da ya faru da Hana muka haka kasa muka rufe ba tare da kowa ya sani ba, daga ni sai ita sai kuma Mama da Kareem da kuma uban gayyar da yayi aikin. Ranar da Baba ya saka ni gaba da tambayar dalilin da ya saka Abdull ya daina zuwa gidan na fada masa ya sake ni ne, Baba tsine min ne kawai be yi ba, amman duk wani kalar zagi na duniyar nan sai da yayi min shi. Musamman da na yi masa karyar cewar kawai bana son sa ne ni na bukaci ya sake ni, kuma da ya bincika sai Abdull ya tabbatar masa da cewar ba fada ba zagi kawai na bukaci sakin ne shi kuma ya aiwatar. Har kusan korata Baba yayi sai da yan'uwansa suka saka baki, Umma ma sai ta koma tana jin haushina domin tallafin da yake bata na sana'ar da Hana bata mata a yanzu ya janye ya daina yi. Sai tace wai bakinciki nake mata saboda ita din ba uwata ba ce, kuma hassada ta bata tsaya kaina ba har da yar'uwata nake yi ma. Ni da Hana ba ma ce mata komai domin mun san abun da bata sani ba. Hana ta samu sallama a yanzu da bata fita siyar da awara domin Mama tana ta shirye shiryen sakata wata makarantar ne a nan garin Kano, hakan ya saka hankalinta ya dan kwanta, kuma wani abun Allah samari da masu mata sai kawo mata hari suke a yanzu. Sai dai ni ban tsira daga maganar mutane unguwa ba, ganin na yi arba'in amman ban koma gidan mijina ba, ba mutanen unguwar kawai ba har cikin family na samu masu jefa min magana wai na ki zaman aure, Mama ta fada cewar wasu daga familyta sun ce haka za a zuba min ida ina aure ina fitowa na ki zaman aure. Na kan yi murmushi kawai na bar maganar a bayan kunnena, domin mai daki shi ya san inda yake masa yoyi, dadi dai ba zai saka mace ta kashe aurenta ta fito domin ta zauna a gidansu ba, ko kuma ta raba a wani guri, ba ni kadai ba mata da yawa al'umma basa musu uzuri, macen bata sakin kanta bata rike kanta amman ba a fahimtar haka, a koda yaushe mutuwar aure yana komawa a bangaren mace idan afku. Ba zan ina cikin jindadi ba, domin zaman gidan ba shi da dadi agaremu. Amman jiki ya dan bude haihuwa ta kara min kyau ta cike min gurbin kasusuwan da na nake da su a wuya, ba wani jiki na yi can sosai ba amman dai jikin ya bude na cika na zama mace. Bayan bikin Zainab na je gidanta na wuni a can muka sha hira sosai na ji abubuwa da yawa da mutanen unguwa suke fada, wasu su ce hakkin Zafeer ne, wannan kam ba zan yi mamaki ba idan aka ce hakkinsa ne, domin ya cutu, wasu kuma suka ce TA KI ZAMAN AURE, har da masu cewa wai Zafeer asiri yayi min ba zan taba iya zaman aure ba, wasu kuma su ce ina da aljannu ne kawai da basa son aure. Na yi dariya sosai na danne ciwon dake zuciyata na bar sirrina a cikin raina. Ta rakoni bakin kofar gidanta ta koma ni kuma na haka hanya gyale na a kafada, kaina ya sha dauri fuska kuma ta dauki ido kamar wata budurwar kai wata budurwar ma albarka domin gyaran da nake yi a yanzu bana yinsa a lokacin da nake budurwa. Ina kokarin tare mai Napep wani dattijo ya faka gabana, ya sauke gilashin motar yana kallona fuskarsa da murmushi. “Ina zuwa?” Na waiga na kalli bayana na kalleshi na yi zaton ko da wata yake magana ba ni ba domin ba yaro ba ne zai haifi kamata da wanda ta fi ni sau goma ma. “Baba ni?” Na nuna kaina, yayi dariya. “Yan mata kenan, shigo na rage miki hanya” “Aa na gode” “Ba zaki shigo ba? To saka min number ki a nan” Ya miko min wayarsa. “Amman lafiya” “Lafiya Kalau Wallahi, kawai na ga ruwan dake min wanka ne, saka min number ki yarinya” Na karbi wayar na saka masa number na, sai ya miko min kudi. “Rike wannan ki hau napep” Na karba na masa godiya, sai ya wuce na bi matarsa da kallo ina dariya, to ko dai ya ga na yi masa kama da tsofi ne ya tare ni haka har da wani ruwan dake masa wanka, tsab kuwa zan masa wankan kwashe kudi na kara gaba domin ba zan iya da kayan majina ba. Allah ya tsare ni. Na tofar da yawu. Ina yin gaba kadan wata motar ta faka shi ma dai sauke gilashin yayi yana min magana. “Hajiya ina zuwa haka?” Na dan taba fuska, yau dai wata kila aljannu sun shafa min maganin farinjini a fuska ko kuma kwaliyar da na yi ce ta dauki hankalin mazan oho. “Gida” Na amsa sai kawai na ga ya bude motarsa ya zagayo ya bude min front seat. “Ki min alfarma motana ta samu lada, na sauke ki gida Hajiya, karki ce aa” Ta ina zan ce aa bayan yace kar na musu, shi din ma be yi kama da wanda za a musa masa ba. Na samu kaina da bin umarninsa duk kuwa da na san ba mutuncina ba ne, na zauna a motar ya rufe ya zagaya ya shiga ya tashi motar. “Sunana Salees” “Noor” “Thank you” Ya fada ba tare da ya kalleni ba, ni kuwa sai satar kallonsa nake baki ne mai dogon hanci ga yalwataccen gashin gemu da zaje gwanin sha'awa. “A ina unguwar take?” Na fada masa, har lokacin be kalleni ba sai da muka shiga cikin unguwar, nesa da gidanmu na ce ya sauke ni. “Baki son na ga gidanku ne?” “Ba kasafai ake kawo ni da mota ba, mutane za su iya wani zaton, kuma Baba baya son haka” Ya juya ya kalleni first eye contact da muka yi gabana ya buga da karfi. “Hakan yana da kyau, tarbiya ce amman da kika san Babanki baya so sai ki kiyaye, abu na biyu ki daina saka veil idan zaki fita, hijab ya fi mutunci, idan kina sha'awar veil ki saka babba wanda zai suturta ki, kina da kyau na zan maza da yawa sun fada miki haka, so ki suturta kyaunki ga wanda yake halalinki haka Allah ya fada” “Na gode zan kiyaye” “Idan kin min izini zan tsaya daga nan har na ga shigarki, saboda zan dawo ko kuma ki saka min number wayarki” Ya miko min wayarsa na karba na saka masa numberta sai ya kira ni. “Ki yi saving number zan kira ki anjima, na gode da kika shiga motata” Na bude na fita ba tare da na ce masa komai ba. Shi kuma yayi reverse ya juya, na ciro wayar a jakata na yi saving number, ashe Kareem ya ga fitowa motar domin motarsa tana fake a gefen gidan makotanmu ne, ban lura ba sai da na karasa, gaba daya sai farinciki ya baibaye ni, ganinsa da na yi. “Laa Kareem baka fada min zaka zo?” “Laa Kareem baka fada min zaka zo?” Ya kwaikwaye ni da wata murya kamar ba shi ba yana mocking dina fuska a hade. “Ba ki da aiki sai raba Number, ki so wannan ki so wannan, ke baki ma san abun da kike so ba, baki san mai son ki ba, ke baki ma gajiya da halin maza ne?” “Haka zan yi ta yi har na dace Kareem” Na fada a shagwabe murya kamar zan yi kuka. “Ba ni wayata” Yana fada be jira na ba shi ya fisge wayarsa dake hannuna ya bude motarsa ya shiga. “To ai line na yana ciki ka ba ni layina” Banza yayi min ya ja motarsa baya ya bar ni tsaye na fara dora hannu a fuska zan yi kuka, ganin hakan ya saka tsaya da motar be tafi ba kuma be yi gaba zuwa inda yake dazun ba, ya dade a ciki sannan ya fito motar ya tako da kafa ya zo ya mika min wayar. “Kalli wani mayafi da kika saka kika fita, haba Noor, kin saka duk raina ya bace Wallahi, idan kika sake shiga motar wani ko kika saka mayafi irin wannan kika fita, ban yafe miki ba, kuma mun bata ba zan sake kula ki ba” Na karbi wayar ina kara bata fuska alamar zan yi masa kuka, i feel so childish when ever I'm near him, da wani ne ya fada min haka ba zan damu ba amman shi na ji babu dadi, kuma abu kadan idan yayi min sai na masa kuka nake jindadi. Motarsa ya koma rai a hade ya bar ni a gurin, sai da ya wuce na duba sai na ga babu liyi a wayar, ashe sim din ne ya cire a motar ya kawo min wayar kawai. Kamar na kwala ihu haka na ji a wane dalili zai karbe min layi ya tafi da shi. Hayaniyar da na ji a zaure ne ya saka ni karasawa cikin gidan da sauri, Hana na zube a kasa tana rusar kuka Baba kuma yana ta zazzaga masifa. “Shiyasa aka boye min, saboda tana auren ubansa, wato kar aka taba mutumcin aurenta ko? Bayan ni kuma ya taba mutuncin aurena” “Me ya faru Hana?” Hana nake tambaya sai Baba ya amsa min. “Munafukar yarinya, daman ai uwarki ta koya miki kiyayya da ni, shiyasa ni baki son farinciki ba ruwanki da damuwa da uwarki kawai kika damu, ashe abun da ya kashe miki aure kenan amman kika boye” “Baba me kake fada?” “Ashe mijinki mutumen banza ne, fyade yayi ma Hana shiyasa kuka rabu, kuma aka boye min? Magana mai girma haka? To ba zan bar wannan ba, Wallahi sai na ja hakkin yata ba zan bari a tafi a banza ba, sai na yi karar ubansa” Na saki wayar hannuna da jakata da mayafin duka suka zube a kasa. “Baba a ina ka ji wannan? Ba gaskiya ba ne sheri ne...” “Sheri? Ai abun duniya baya boya ina zamana wata mata ta zo ta fada min” Na dafe kaina. “Innalillahi Wa'inna Illaihirraji'un, Baba ba gaskiya ba ne, kawai na gaji da zama da shi ne muka rabu” “Kika sake magana sai na tsine miki albarka ma, har matar da ta cirewa Hana ciki na ganta da idona na yi magana da ita, kuma ba zan bar maganar nan ba” Hana ta girgiza min kai tana kuka ni ma kukan na fara Umma kuma ta saka salati yana tabi da rike baki... Pay 500 to 2451879008 Zenith Bank Hadiza Abubakar And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.Ya rigata isa domin shi yake son magana da ita a yanzu, a yanzu ikon a gurinta yake hakan ya saka ta bata masa lokaci na tsawon mintuna arba'in sannan ta shigo gidan. Yana tsaye ta window falon yana kallonta har ta fito motarsa ta turo kofar falon ta shigo. “Lafiya kake son ganina?” “Me kike so Safeena” Kamar jira take sai ta sauke gyalenta ta aje jakar a kujera ta nufo shi tana nuna shi. “Kai Kareem kai nake so!” “To miye matsalarki da Noor? Miyasa kike cusata a cikin matsalarmu?” Ya tambaya ba tare da ua juyo ba hannayensa duka biyu suna zube a aljihunsa. “Saboda Noor ce ta raba ni da kai, Noor ce macen da ta cike gurbina da ita, kuma ita ce ta kashe min auren da takardar kawai ya rage Abdull ya ba ni” “Ban cike gurbinki da na noor ba, wani gurbi na gina mata mai kyau mai tsabta, mai cike da kauna da soyayya, dan Allah ki cireta a cikin matsalarki” Har lokacin da yake maganar be juyo ya kalleta ba. “Ita ce babbar matsalata a rayuwar nan Kareem, ta lalata min aure tun da mijina ya dauki yaran nan ya tafi da su ya auna jininsu be sake dawowa gidan nan ba, last week ya aiko kanensa ya dauki yaransa biyu aka bar karamin da na haifa da kai, yanzu haka mijina yana garin nan amman be tako kafarsa gidana ba, ya daina min aike ya daina kulani baya amsa wayata baya ba ni amsar sakona, na sani saki na zai yi bayaj ya gama kwance min zane a kasuwa, zai saka kowa ya tsane ni a danginmu saboda abun da na aikata Mijina cousin dina ne, kuma duk sanadin Noor ce ne domin ita kadai ta san sirrina ita kadai zata iya fallasa wannan” Ya juyo ya kalleta. “Ta aikata kuskure na fahimta, mu ma mun aikata dukanmu mutane ne, amman saboda me zaki lalata rayuwar kanwata me ya shigo da kanwarta ciki? Kina da tabbacin Abdull din ne ya aikata?” Ta matsa kusa da shi tana masa wani kallo na tsana for the first time. “To waya aikata kai? Ko kuma dai ita ta aikatawa kanta?” “Baki da tabbacin Safeena karki jefa rayuwarki a matsala” Ta yi wani shu'imin murmushi. “Na san komai Kareem kai ka san wacece ni, ina da tabbaci mana, a gabana ka kira kawata ina jin muryarka lokacin da kake fada mata cewar wata yarinya kake son ta yi ma wankin ciki ka mata allura amman dai ka fi son a wanke saboda ka samu tabbacin komai ya zube, ka fada mata kaddara ce ta hau kan yarinyar fyade aka yi mata ko ba haka ba?” “Ita Juwairiyya ce ta fada miki haka?” “No Wallahi bata fada min komai ba, amman na ari wayarta na duba bangaren kira sai na ga number ka, daman kuma na ji muryarka domin wayarta ana ji duk abun da mutum ke fada sound din kiranta a karshe yake, lokacin da na duba zuciyata ta fada min Hana ce, there is no way da zai saki Noor da ciki ba tare da wani abu ba, kuma ya fadawa yan'uwansa wai ta tayar masa da fitina ne sai ya sake ta shi kuma ya sake ta saboda TA KI ZAMAN AURE, kana ganin hankalina zai dauka? Idan babu wani abu me zai saka Noor ta fada masa cewar dan da na haifa ba na shi ba ne? Mw zai saka yar'uwarta ya yanke karatunta da duk wani gata da yake musu ta dawo ita da kanwarta su zauna a gida? Daman ni ban yarda ba na san akwai wani abu a kasa, domin na san waye mijina ba kasafai yake iya rike kansa ba, a tsawon watanin da yake a Lagos da sunan aiki na san me yake aikatawa, kawai na zuba masa ido ne saboda babu yadda zan yi, kana tunanin namiji zai saka al'adar neman mata a gaba kamar yadda Abdull yake kuma ace matarsa bata sani ba?” Ta share hawayen da suka zubo mata cikin daga murya ta cigaba da fadar. “Neman matansa ya taimaka min gurin bibiyarka da kokarin kulla alaka da kai Kareem, na san yana neman mata tun kamin na aure shi, na aure shi ne saboda an matsa min a gidanmu na yi aure, kai kumaka guje ni, duniya ta min zafi, shi kadai ne mutumen da ya zo zai share min hawaye a lokacin, bayan mun yi aure ya zama bana burge shi saboda ya saba da matan waje, mijina ba shi da lokacina, baya ganin kyauna, ba ya ganin ado na, kullum idonsa akan matan waje ne, mijina baya iya gamsar da ni yadda kake min Kareem, gaba daya ban yi dacen rayuwa ba, amman a haka nake zaune kullum burina idan har na bar Abdull kai ne” Wannan karon da cinyar hannu ta goge hawaye idonta na dama. “Na san na yi kuskure na haihuwar ba ta sunna ba, dukanmu yin yi kuskure amman sai mu rumgumi wannan kaddarar, nan gaba kadan Abdull sakina zai yi, to sai ka aure ni mana Kareem” Ya juyo da kyau ya fuskance ta. “Ba zan taba aurenki ba, amman zan tabbatar maki da abu daya, Noor ba zata aure ni ba, saboda bana cikin mazan da take so, please ki cireta a cikin matsalarki” “I don't care ka auri Noor ko karka aureta ba matsalata ba ce, abun da kawai na damu da shi, shi ne idan Abdull ya sake ni zaka aure ni” “Har abada ba zan taba aurenki ba, aure ya haramta a tsakaninmu” Ta rausayar da kai tana murmushi. “Na fahimci hakan ai, shiyasa na bullowa ubanta ta wannan sigar na fada masa gaskiya kuma na kwadaita masa dukiyar da zai samu idan ya Abdull ko mahaifinsa suka bukaci a sirrinta abun, na samu wata kawata muka je a zuwan ita ce nurse din da ta cire ciki, kuma na samu kudi mai kauri na ba shi. Ka ga yanzu hankalin Abdull zai koma gurin abun da ya aikata ne ba wanda zai aikata a gareni ba, kuma idan ya fallasa sirrina duniya zata zage mu a gaba dayanmu mu uku, kai ni da kuma shi” Kareem ya sasauta fuskarsa ba dan tsoron furucinta ba sai dan yana son ta fahimcin illar fa hakan zai mata ba mijinta kadai ba. Ya busar da iskar bakinsa ya jin kirjinsa na ciwo sosai. “Ki rika yin tunani kamin ki aikata abu, kina da yaya Safeena, tun farko baki rike aurenki kika biyewa shaidan muka aikata alfasha, hakan be wadatar da ke ba sai da kika ga mun haihuwa, yanzu gashi abun ya dawo yana bibiyarmu, kuma duk yadda wannan abun zai taba ni be kai yadda ke zai miki illa ba Safeena, saboda ke mace ce ni kuma namiji ne, shiyasa da Allah zai ambacin mazinata a kur'ane sai ya fara da mace, domin ita ce mai rauni kuma ita ce mai shiga kaso 90 na matsala sama da namiji” “Zaka aure ni Kareem? Ka min alkawari kawai zaka aure ni Wallahi zan yi duk yadda zan iya mahaifinta ya janye shari'ar nan” Ya cire hannunsa daya a aljihu yana nuna mata. “Let me make this clear to you, idan har zan sake wani aure a rayuwata, to mace daya ce zan aura Noor, idan har ba zan auri ba ba zan sake aure ba, so ki saka a ranki ni da ke ba mu taba sanin juna ba, ba zan taba aurenki ba Safeena!!” Wani mugun kallo take masa zuciyarta na bugawa da karfi. Cikin ihu da takiya ta ce “Ba zan saka ya janye shari'a ba Kareem kuma zan daukar masa lauya, domin ina bukatar abun da zai daga hankalin Noor ya zubar da mutuncinta da na iyayenta ya kashe auren uwarta ya jafata a matsala, ba ni da makiyaya a duniya irin Noor yarinyar da saboda ita igiyar aurena take rawa? Saboda ita juya min baya, yar sikar yarinya shashasha mahaukaciya, yarinya da bata kai ta goge talkamin kafata ba, yarinyar da bata kai ka rika hannunta ba, amman ita kake so? Yarinyar da ubanta baya jin wani yare sai na kudi? Yarinyar da ubanta be san wani mutuncin ba sai na kudi? Yarinyar da babu komai akanta sai hauka da gidadanci, fasika da bata iya komai ba sai bibiyar mazan mutane yarinyar da...” Tassssss ta ji saukar lafiyayyen mari a fuskarta daga hannun masoyinta Kareem, Wani irin numfashi taja da karfi ta kai hannu ta dafe kuncin hawaye masu zafi na sauko mata. Cikin wani irin bacin rai da Kareem be san yana da shi ba ya nuna ta da yatsa ya ce. “Kul bakinki ya sake kiran Noor dita da wata kalma marar kyau, iyakar kiyayar da kike mata saboda tana da alaka da ni ne, ni kuma ba aurena zata yi ba, ki fadawa mahaifinta karya kike ya janye shari'ar nan idan ba haka ba...” Wayarsa ta yi ringing ya ciro wayar ya duba farincikinsa ce take kira wato Noor, ya amsa wayar ya kara a kunne shi ma dai sound din kiransa a karshe yake kamar yadda na mutane da yawa yake a manyan wayoyin yanzu. “Kareem ka yi magana da Baba? Me ya fada maka?” Sai da yayi iya yadda zai ya danne yakin dake zuciyarsa ya amsawa Noor da murya mai sanyi. “Na yi magana da shi be yarda ba, amman zan sake samun shi gida mu yi magana karki daga hankalinki” “Ki kwantar da hankalinki ko?... To yaudararki yake yi yarinya, ke ma amfana zai yi da jikinki ya jefar da ke kamar yadda ya jefar da ni ki bi sannu...” Safeena ta fada da karfi, Kareem yayi hanzarin kashe wayar, fuska a hade ya jefawa Safeena mugun kallo da idanuwansa da suka gama canjawa. Wani marin ya sake kai wata, ya saka kafarsa ya kwashe nata kafafuwan sai da ta fadi kasa, ya daga kafarsa ya daki bayanta sai da ya amsa, sannan ya cire belt din jikinsa ya fara zuba mata ba ji ba gani... Duka yayi mata sosai kamar wani ubanta sannan ya fice ya barta a gurin tana ihu tana kuka. Motarsa ya shiga ya kama hanyar tafiya ganin yarsa domin ya san a yanzu su kadai suke rage masa, aikin ma baya jin zai iya tafiya a yau tun tashinsa baya jin lafiya balle kuma yanzu da abubuwa suke juye masa. Sai da ya shiga unguwa ya ji ba zai iya karasa family house dinsu ba, nesa da gidan ya faka mota ya kwantar da kujerarsa ya jinke hannunsa ya rufe ido yana nadamar dukan da yayi ma Safeena, domin be tana kai hannunsa yayi ma mace duka irin wanda yayi mata a yau. Yana cikin motar ya aka kira sallah azahar sannan yaja motar daker yana jin kansa na ciwo kamar zai tsage gida biyu ya isa masallacin unguwar yayi sallah ya sake komawa motarsa, sannan ya karasa gidansu. A harabar gidan ya faka motar ya kashe yana kallon flowers din da suke gabansa amman zuciyarsa tana can wata duniyar. Wayarsa ya ciro ya duba number Noor ya sauke ajiya zuciya ya kai sau takwas sannan ya danna na aika mata kira cikin tsoro jikinsa har rawa yake. Shiru yayi bayan ta daga kiran, sai kuma ya rasa me zai fada mata, ya zai fara mata bayanin komai ya zai wanke kansa, ta ina zai fara fahimtar da ita, be ma yi tsammanin zata amsa kiran ba. “Karka sake kirana Kareem, karka sake zuwa kofar gidanmu, na zan sake karba ko neman wani taimako a gurinka ba, matsalata da ta yan'uwana tawa ce zan ji da kaina, na yanke alaka da kai har abada...!” “Noor” Zai yi magana ta yanke kiran, runtse ido yayi sosai, ne bude ba sai da ya ji an bude gate din gidan, direban dake dauko yaransa daga makaranta ne ya dauko su ya faka a inda ya saba faka motar. A yake Kareem ya nemo kwarin guiwa da juriya ya sakawa zuciyarsa ya bude motar ya fito cikin karfi hali yake takawa yana murmushi ya nufi yaransa da suka nufo shi suna. “Oyoyo Dady Dady Dady” Kamin ya karasa gurinsu su ma su karaso gurinsa ya yanke jiki ya fadi kasa ribbbb. “Dady.....!” Tine ta saka ihu ta saki bag dinta da lunch box din dake hannunta ta kama mahaifinta tana kiran. “Momy Hajiya... Anty Khadija... Yaya Aaryam... Dady na ya fadi... Dady...” NOOR POV. Sai da na zabura a lokacin da yayi hanzarin yanke wayar, kenan yana tare da Safeena har yanzu? Kuma yake fadar yana so na? Yake fadar ya tuba? Yake fadar yayi nadama? Me ya kai shi gurinta? Me yasa ma zai amsa wayata a gabanta. “Ki kwantar da hankalinki ko?... To yaudararki yake yi yarinya, ke ma amfana zai yi da jikinki ya jefar da ke kamar yadda ya jefar da ni ki bi sannu...” Maganar Safeena ta sake nanata kanta a kunnena, zai iya zama gaskiya shiyasa dazun ya daure ni da kalamansa, namiji zai iya aikata komai domin ya samu biyan bukatar kansa. Na mike tsaye zuciyata na raya min Safeena ce matar da Baba yace ta same shi da maganar, ita kuma ta ji ne ta gurin Kareem. Ya fada mata sirrina kamar yadda ya fada min nata, me yasa yake haka? So yake ta jefa ni a matsala ta yadda zan rasa kowa sai shi kadai shiyasa yake taimako na a ko da yaushe? So yake na rasa kowa na zama tare da shi shi kadai, shi kuma sai ya juya ni a yadda yake so? Yanzu na gane dalilin duka taimakonsa na gane manufarsa, na gane buri da bukatunsa. Sai bayan Sallah azahar sannan kiran Kareem ya shigo wayata, na sani daman zai kira ko ya zo domin kare kansa, kuma na shiryawa duk wata karyarsa sai na ga iya gudun ruwansa. Na amsa kira sai yayi shiru ba tare da ya ce komai ba. “Karka sake kirana Kareem, karka sake zuwa kofar gidanmu, na zan sake karba ko neman wani taimako a gurinka ba, matsalata da ta yan'uwana tawa ce zan ji da kaina, na yanke alaka da kai har abada...!” Na fada masa kai tsaye hawaye na zubo min zuciyata na zafi because this is the most hardest words i had ever said to someone, who's there for me in every Situations, rabuwa ce irin wanda rai be so ba amman dole na yi. “Noor...” Zai yi magana na yanke kiran ba tare da na tsaya na saurari abun da zai fada ba. Na dafe zuciyata ina kuka he's someone who's  always been a good friend to me, but the fact that i know yana da manufa na yin haka ya yanke duk wani hanzari, ya ture duk wani uzuri nasa, ba zan iya yarda na lalata rayuwa saboda namiji ba. Karfin hali na yi na fita na siyowa Hana maganin zazzabi domin jikinta yayi zafi sosai fever ya rufe ta. Ana gama sallah la'asar ban tsaya cin abincin rana da Umma ta sauke ba na yi mata karya cewar Zainab ta kira waya na kaiwa mahaifiyarta su yi magana saboda wayar mahaifiyarta ta lalace. “Ki dawo da wuri, domin Babanki tun da ya fita be dawo ba har yanzu kin san kuwa yana hanya a yanzu, idan ya dawo be same ki ba, ke ce a ruwa” “Ba zan dade ba In Shaa Allahu” Na saka talkamina ina kara sirranta jakata dake boye a hijab dina na fice daga gidan, kai tsaye titi na nufa daman manufar ta samu dalilin fitar ne. Ina kokarin taron Napep na muka yi ido hudu da Zafeer zai karya kwanar gidanmu da wata kafirar mota mai kyau da kyalli. Wuce ni yayi ya shiga kwanar ni kuma na shiga Napep din na fada masa inda zai kai ni, yana tafe ina mamakin mi ya kawo Zafeer a nan ya domin tuni ya dauke iyayensa daga unguwar saboda likkafa ta yi gaba a wata unguwa mai kyau suke zaune a yanzu. A kofar gidan Abdull kuma gidan Safeena mai napep din ya sauke ni na bashi kudinsa na shiga gidan bayan mun gaisa da mai gadin, har yake fada min bata dade da shigowa gidan ba. Da manifa biyu na zo gidan an roketa alfarma ta saka mahaifina ya janye ko kuma na yi mata ta karfi. A bakin kofar falon na tsaya na bude jakata na dauko wayata na sakata a airplane mode sannan na kunna recording na shiga falon ina sallama, wayar na rike a hannuna. “Wa'alaikumussalam, bakar macijiya me kuma ya kawo ki?” Ta amsa min tana tsaye rike da maganin da ban san na miye ba a hannunta, fuskarta ta kumbura daga bakin inda yake ina kallo a jikin, fuskarta da kafadarta zuwa kafafuwanta da hannunta sun yi ja, alamar an mata duka. “Magana na zo mu yi dan Allah ki saurare ni Safeena” “Ina jinki” Na matsa kusa da ita na fara mata magiya da raunaniyar murya. “Idan kina tunanin wani abu ne a tsakanina da Kareem, Wallahi babu dan Allah dan girman Allah ki yi hakuri da abun da na yi miki, ina rokonki alfarma ki saka Baba ya janye shari'ar nan” “Ashe kin san kin cutar da ni, wato yanzu kina son mu sasanta dan kar auren uwarki ya mutu kuma asirin kawarki ya tonu ku kunyata ko? Amman ke kika son kunyata ni, ki bara ni da abun da nake so, kin yi iya yadda kika iya har sai da kika fitar da ni a zuciyar Kareem, hakan be miki ba sai da kika auri mijina, hankalinki be kwanta ba sai da kika fada masa cewar dan da na haifa ba jininsa ba ne” “Cikin fushi na fada masa hakan, kuma ba dan ya sake ko ya juya miki baya ba, kawai na fada ne saboda a lokacin raina yana bace ne, na bakinciki abun da yayi ma kanwata” “Ai kin ci riba idan bibiyar mazan mutane yana da kyau kin gani ai, kin gaji kwadayi gurin ubanki, gaba daya kin firgita min tunani, kin saka Kareem ya tsane ni mijina ya tsane ni, mijina yana garin nan amman ya ki ya zo gidana, yau kuma Kareem yayi min abun da be taba ba, kin saka masa wani banzan hali da ba na shi ba, na tsane ki Noor” Na risina kasa ina rokonta. “Dan Allah ki taimaka min Safeena, Wallahi ba zan fadawa kowa cewar kin haihu a waje ba, dan Allah ki fadawa Baba karya kike ya janye shari'ar nan” “Fadi na nawa kuma, ai kin gama fada tun da kika fadawa mai gayya mai aiki, kin fadawa Abdull ya sani to miya rage? Wato Kareem fada miki ni na fadawa mahaifinki haka ko? To be yi karya ba ni na fada, ni kuma shi ya fada min, ki daina biye masa kina yaudarar kanki ni dai na riga na harbo jirginsa, kuma babu abun da za a fasa idan kina son ubanki ya fasa shari'a to ki fadawa Kareem ya aure ni, ya kyale ki shikenan nake bukata sai ki samu salama idan ba haka ba kin fara ganin matsala kenan a rayuwarki tafi ki bar min gidana” Ta fara turani, sai na tashi na share hawaye na fice daga falon, ban yi nisa da gidan ba na shiga contact list din na whatsapp na tura mata recording din da na yi saving sannan na buga mata warning. “Ko dai ki fadawa Baba karya kike ki karyata kanki, ko kuma na tura audio nan a gurin surukarki da mahaifin mijinki da kanensa kuma da gaske nake na baki daga yau zuwa gobe” Ina fitowa na cire airplane mode din na kunna data da domin sakon ya samu isa, sannan na tari Napep na shiga, gidan Mama na nufa domin labarta mata halin da ake ciki na tabbatar bata san wainar da ake soyawa ba, idan har ta sani zata kira ta fada min ko ta tambayi wani abu, wata kila ita ma idan ta saka baki Baba zai aminta ya sauko. Sai dai na yi rashin sa'a ban same ta a gidan ba, sai mai aikinta na samu tana kallo a falo. Ruwa kawai na sha na kira wayar Mama, ta amsa ni ta fada min bata gidan tana gurin gaisuwa wata kanwar mijinta mahaifin Abdull ce ta rasu. “Mama idan kin dawo ki kira ni akwai maganar da zamu” “Ki jira na dawo, lafiya na ji yanayinki haka?” “Mama bari sai kin dawo” Kiran Mama na yankewa, sai ga kiran Baba ya shigo wayata ina dauka ya fara zagina yana tambayar ina na tafi. “Ina gidan Mama” “Maza maza ki dawo gida yanzu nan” Na mike tsaye babu shiri na yi ma mai aikin sallama na fice. Tare muka fito gidan da Abdull yana cikin motarsa ni kuma ina tafiya a kafa, ban yi mamakin ganinsa ba domin gidan ubansa ne, kuma Safeena ta fada cewar yana gari. Sai dai abun da ya ba ni mamaki kuma ya tsorata ni a lokaci daya tsayar da ni da yayi yana son magana da ni, ashe karfin halin maza har ya kai haka. “Magana ce kawai zamu yi Noor dan Allah ki shigo” Na yi kamar ban san da wanzuwarsa a duniya ba domin babu wanda na tsana irinsa kallonsa ma idan na yi bakinciki nake ji. “Zamu yi magana ne akan karar da mahaifinki ya shigar, ina nan ya kawo sammaci, magana ce da zata sama mana masalaha gaba dayanmu” Na tsaya wata idea na zo min, sai na saka wayata a recording kamar yadda na yi dazun idan na samu yadda nake so, zan iya mixing abubuwa su tafi yadda nake so. A gurin da na tsaya ya faka motar ya bude min front seat. “I know you hate me but please ki shigo mu yi magana magana ce ta sirri” Na kalli gurin sannan na shiga na zauna. “Na ga shigowarki, na so na miki magana amman na san ba zaki saurare ni a lokacin ba, shiyasa na jira har kika fito” “Ka ce zamu yi magana akan abun da ya shafi Shari'a ne ba wani abu ba, idan baka ka abun fada zan fita” Na fada a tsawace jikina har bari yake ji nake kamar ace akwai wuka kusa da ni na caka masa. “Akan shari'ar da mahaifin ya shigar ne, baki tunanin hakan zai iya shafar ki ya shafi kanwarki? Ni fa ban aikata komai ba? Wane tabbaci kike da shi cewar ni na yi mata fyade?” Na dube shi. “Baka aikata ba karya ake maka?” Sai yayi saurin dauke idonsa. “Na ji na aikata, amman ai kaddara ce da bata wuce kowa ba, kuma ke kin san ba zan amsa wannan a kotu ba, kuma baku da wata shaida, na san ubanki ya shirya haka ne saboda kwadayi irin nasa, zan bashi kudi enough, ya janye karar nan karya bata min suna ni da mahaifina, abun da zai biyo baya ba zai muku dadi ba” Kalaman da suke fitowa bakinsa sun karfafa min guiwar aje wayata a cinyata fa yadda sautin zai samu daukuwa da kyau. “Sannu namiji wato har kana da baki da karfin halin da zaka min bazarana kuma ka cilasta ni ko mahaifina, bayan duk abun da ka yi? Ka keta haddin kanwata har ka yi mata ciki sannan ka kalli kwayar idona ka yi min barazana Abdull...!” “Baku da wata hujja akan hakan, kuma fitar wannan zancen zai zubar mata da mutunci ne kawai, dan haka ki natsu ki tattauna da mahaifinki mu taru mu rufawa juna asiri, idan wani abu yake so zan ba shi” Kiran mahaifina da kwadayayyen da suke ya fi komai kona min rai sai dai babu yadda zan yi domin Baba ne ya budewa kowa kofa. Sam na manta da ban saka wayata a airplane mode ba, sai da kira ya shigo wayar. Wayar ta kawo haske kiran yayi appearing saman screen recording din kuma daga tsayaki daman wayar ba a key take ba, tun da Kareem ya ba ni ita ban saka mata password ba. Na yi hanzarin daukar wayar amman hakan be hana shi gani ba, daga Safeena da take kira har zuwa Recording din da nake. “Recording kike? Ina kika dosa Noor” Na bude motar na fita da sauri sai ya bude ya zagayo kamin na yi wani yunkuri ya kamani da kokawa ya murde min hannu ya karbe wayar. “Ka ba ni wayata Abdull” Be kula ni ya rufe gefen da nake tsaye ya zagaya zai shiga motarsa na bishi ina fadin ya ba ni wayar. “Ka goge recording din ka ba ni wayata” Be kula ni ba ya rufe motar yayi mata key ya bar ni a gurin tsaye cikin bakinciki da nadama. Why I'm such a fool and idiot me yasa ma na yarda na yi magana da shi, no wait me yasa ban saka wayar a airplane mode ba kamar yadda na yi dazun. Da kafa na taka na isa Family house din su Mama, a gidan na kwana gaba daya na rasa ya zan yi kuma na san idan na koma gida Baba zai rufe ni da fada ne wata kila har da duka. Abun da ban sani ba, ashe bachin da na yi a gidansu Mama na tsira ne, bachin na chanji ne daga wata kaddarar zuwa wata, ashe na bude wani sabon babin ne na kaddara, domin na wayi gari da mummunan labari...