❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) ⚘🕊 MALLAKIN MEERAH 🕊⚘ 【 CUTIE PIE 】 Marubuciyar littafin :【 TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 】 YOU CAN FOLLOW MY WHATSAPP CHANEL 👇👇👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK .............. 2 🌹👑 THE ROYALTY LOVE ✌👑🌹 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 1 ❤🔥 DAULAR SAUDIYA 🔥👑 Tarihin kassar saudiya a matsayin kassa ya fara ne a karni na 1727 da hawan Malik Al Saud wanda ya kafa masarautar Saudiya wanda kuma shi ne sarki na farko a saudiya , wannan yankin an san shi da tsofin al'adu da kuma na zamani , ya na da mahimmacin ga alamun ayukan dan Adam na farko, Musulimci wanda ya kunno kai a karni na 7 , ya ga saurin fadada sauran yankunan bayan mutuwar Muhammad ( S.A.W ) a shekara ta 632 , wanda ya kai ga kafa daular larabawa masu tasiri Yanku na hudu su ka kafa saudiyya ta zamani : Hejaz , Najd , Gabashin Arabiya , da Gudancin larabawa , wanda ABDOULAZIZ BIN ABDOUL RAHMAN ( IBN SAUD ) da ga Al Saud ya hade a 1832 inda ya kafa saudiya a cikakiyar masarauta wanda ya hau mulkin ta , gano man fetur a shekara 1838 ya mayar da shi babban hako A shekara ta 1840 yanku nan hudu bisa jagoranci uban gida jen su , su ka nemi hawa Mulkin saudiya baki Dayan ta, Hakan ko ya tada wani gagarumin yaki a tsakanin masarautar nan hudu , Daular Ottoman da ta kafu tsakanin yankin Hejaz da Gudancin larabawa bisa shugabancin AHMED ABU-TALIB , sannan Daular Saudiya da ta kafu tsakanin yankin Najd da Gabashin Arabiya bisa Shugabancin ABDOULAZIZ IBN SAUD Sun yi gagarumin yaki wanda Daular saudiya ta fito a matsayin mai nasara sakamakon Manya manya warriors din ta , wanda ba su ja da baya a kashe ko akashe su ABDOULAZIZ IBN SAUD ya hau mulkin Saudiya baki daya wanda kuma ya hau a matsayin shugaban kassar , duk wasu shawarwarori na administration a hannun sarkin Saudiya ta ke ABDOULAZIZ BIN SAUD ya na da diya uku biyu mace dayan namiji ZAYD ABDOULAZIZ BIN SAUD wanda ya hau mulkin Saudiya Bayan rasuwar mahaifin shi a 1883 Bayan hayan ZAYD BIN SAUD Daular saudiya ta kara habaka , duk wasu masarautu da su ke Gabashin Saudiya da Arewacin ta da Yammacin ta duk saida su ka dawo a karkashin mulkin Daular Saudiya , Banda Gudancin wanda ke hannun Daular Ottoman Bayan Hawan Mulkin ZAYD BIN SAUD ya auri mata hudu wanda su ka fito da ga gidajen saurata da ke karkashin Daular Saudiya , ta hudun kuma da ga Daular Ottoman dan rage tsananin da ke tsakanin wadanan Daular hakan ko ba karamin tasiri ya yi ba dan tun bayan hakan zumunci ya kulu tsakanin wadanan gidan sarauta biyu cikin wani ikon ubangiji duk cikin matan ZAYD BIN SAUD Gimbiya Hindi ta Daular Ottoman kadai ta haifi yaron ta daya tilo namiji , duk ukun Mata ne su ka haifa A shekara ta 1948 ABDOUL LATIF BIN SAUD da tilo ga ZAYD BIN SAUD ya hau karagar mulkin DAULAR SAUDIYA bayan rasuwar mahaifin shi da mahaifiyar shi sakamakon wani hari da yan leken asiri su ka kai musu a cikin masarautar a lokacin ya na da shekara 26 Bayan hawar garar mulkin ABDOUL LATIF BIN SAUD ya auri mata Biyu , ta farko Gimbiya HOUDA da ga masarautar Rouma , da kuma Gimbiya YOUSRA da ga masarautar Jordan Cikin wani ikon Allah Duk yaran da su ka haifa mata ne , ko wace sai da ta haifi yara mata biyar amma babu namiji Amma duk sauran yara mata na ZAYD BIN SAUD da su ka auri Manya Manyan yan kasuwa da kuma yaran sarki sai da su ka samu da namiji Banda ABDOUL LATIF BIN SAUD A shekara ta 1985 MALIK ABDOUL LATIF BIN SAUD ya auri matar shi ta uku Gimbiya DJAOUDATT da kudurin ta samar mishi da namiji wanda zai gaje shi Amma ita ma Gimbiya DJAOUDATT diya mata kawai ta haifa Ganin yadda shekaru su ka ja ya sa MALIK ABDOUL LATIF BIN SAUD yanke shawarar duk cikin yaran shi mata , wadda ta fara aure , mijin ta zai zama MALIK a bayan ran shi Cikin wani ikon Allah Autar ABDOUL LATIF BIN SAUD Gimbiya INAS diyar MALIKAT DJAOUDATT ta fara fido da mijin aure a lokacin ta na da shekara 18 Ba a bata lokaci ba MALIK ya aurawa Gimbiya INAS wani yaron babban dan Kasuwa a cikin masarautar Saudia HICHAM BIN JAABAR Shekara uku bayan auren su su ka haifa kyakyawar diyar su mace wadda ta ci sunan RIANNA BIN JAABAR Sati daya bayan shigowar ta duniya MALIK ABDOUL LATIF BIN SAUD ya bar duniya shi kuma , MALIK HICHAM BIN JAABAR ya hau karagar mulki Amma bayan hawan shi mulki ba su kara samun haihuwa ba shi da MALIKAT INAS Abun ya janyo kananan magaganun a cikin masarautar baki daya , hakan ya sa MALIK HICHAM BIN JAABAR yanke shawarar karo aure A wannan karan kuma ya auri Gimbiya MOUSSINA babbar y'a ga ABDOUL MUJEEB BIN AHMED sarkin Daular Ottoman a lokacin Cikin wani ikon Yaron su na farko da namiji ne wanda ya ci sunan AMIR NAWFEL Shekaru shida bayan shigowar shi duniya su ka sake samun yarinya mace mai sunan AMIRA TESNIM da ga ita ba su sake samun haihuwa ba Bayan AMIR NAWFEL ya cika shekara 18 MALIK HICHAM BIN JAABAR ya gabatar da shi a matsayin magajin shi , MALIKAT MOUSSINA kuma ta zamo MALIKAT AL'UMU wato mahaifiyar yarima mai jiran gado wanda karfin ikon ta ya fi na MALIKAT INAS Duk wanna abun da ke faruwa Daular Ottoman na gefe na kallo su na jiran lokacin buga game din na su dan har yanzu ba su hakura da mulkin saudiya baki daya ba , a wannan karnin mulkin saudiya dole zai koma hannun Daular Ottoman ( TSAGAITA CEN LABARI A KAN DAULAR SAUDIYA DAN KAR KU RIKICE DA GA GABA , ALLAH YA SA KUN GANE YAWWA 😴😴😴🤙 ) SIX YEARS BEFORE DAULAR SAUDIYA 🔥👑 * AMIR NAWFEL Zaune ya ke cikin wani katafaren garden kun san yadda gidajen saurata su ke , musaman masu mulki da kudi to be sai na kai ga yi muku wasu bayanai ba Ya na sanye da wasu kaya masu bala'in kyau irin na sarauta ya daura wata Alkyaba fara kal da ga sama Ya na zaune saman wata sofa mai mugun kyau da laushi , gaban shi kuma wata table ce ta glass shake da fruits da juice , ga uban dogarai a zagaye da shi ta ko ina ko wane ya na rike da wata katuwar sword kamar wanda za su yaki Shi kuma AMIR NAWFEL ya daga kan shi sama ya lumshe idanun shi kamar mai tunanin wani abu AMIR NAWFEL hadaden namiji ne , Fari kal da shi kamar ka taba jini ya fito , ya na da dogon hanci kamar pencil , da dan karamin baki , lips din shi red colour ne , shape din na sama ya firo kamar heart , ya na da gashi sosai so smooth mai laushi kuma baki kirin da shi har wani kyali ya ke yi da ga gani ka san ana kula da wannan gashin , ga wani kontancen saje a geffen fuskar shi , a shekaru zai kai 24 haka A geffen wuyan shi na dama ya na da wani bakin zane ya fito kamar crown an dasa mata Sword a tsakiya , allamun tambarin masarautar ne Ya na a haka ya ji daura mishi kai saman cinyar shi Dan karamin murmushi ya saki dan ya san ko wanene , a hankali ya ware idanun shi ya na kallon sama kafin ya sauko da kan shi slowly Ya na da dara daren idanun idanun farare kal kamar madara , kwayar cikin su kuma Hazel ce mai bala'in kyau kamar mirror Cikin wata irin zazzakar Murya cike da nitsuwa ya ce " what are you doing here ? " ya fada da turanci Wata kyakyawar yarinya ce fara kal da ita cikakiyar balaraba , kamanin ta daya da AMIR NAWFEL sai dai ita launin idanun ta baki ne kal a shekaru ba za ta wuce 17 ba , Al-AMIRA TESNIM kenan , Auta ga Malik HICHAM BIN JAABAR Cikin shagwaba ta fara magana da harshen larabci ta ce " Akhie , wai yaushe za mu tafi wajen papi ne " Hannun shi ya daura saman kan ta ya na shafawa a hankali Sai da ya dauki lokaci ya ce " za ki iya tafiya ni dai ba zan je ba " Ya na gama fadar hakan ya meda kan shi saman ya lumshe idanun shi Dago kan ta ta yi , ta mike zaune ta na kallon shi ta ce " uhumm uhummm Akhie ni fa........ " Da sauri ya daga mata hannu ya katse ta , a hankali ya ware idanun ya sauko da kan shi kassa kafin ya mike ya fara takawa ya bar wajen ba tare da ya ce mata komai ba Da sauri wasu dakarai guda hudu su ka bi bayan shi , ya bar yarinyar nan zaune da sauran dakaran , sai faman hura hanci ta ke AMIR kuma a hankali ya ke tafiya cike izza kai a sunkuye , da ga ganin takun shi ka san izza a jinin shi ta ke Ya na tsaka da tafiyar shi , wata arrow ta fado dab da kafar shi cak ya tsaya , Kallon arrow din ya yi na dan lokaci kafin ya duka a hankali ya dauke ta ya na bin ta da kallo A hankali ya saki wani cool murmushi , ba tare da ya dago kai ba ya ce ma dakarun shi su je su bashi wuri Sunkuyar da kai su ka yi cikin girmamawa kafin kowane ya juya ya koma bakin aikin shi Su na barin wajen ya dago kai ya fara bin wajen da kallo , amma bai ga komai ba A hankali ya ci gaba da takawar shi har ya nufi wani dan building mai mugun kyau , ga wasu jibga jibgan dakaru zagaye da wajen Ya na isa wajen duk dakarun su ka zube saman guyiwowin su su na gaishe da shi Bai bi ta kan gaisuwar su ba ya shiga wajen kai tsaye ya na sallama kassa kassa babu wanda ya ji ta sai shi da ya yi abun shi Ya na shigowa wajen idanun shi su ka sauka kan wata mace sanye da wando palazzo Fari kal da riga ita ma fara ta na da madauri da ga tsakiya , ta saki wani lalawsan gashin kan ta baki kirin har tsakiyar bayan ta Ta juyawa kofar shigowa baya , ta na kallo ta cikin wata katuwar Window ta glass A hankali ya ci gaba da takawa , ya sa hannu ya cire alkyabar shi ya ajiye saman wata table ya daura arrow din a sama Kamar ta san da shigowar shi , ba tare da ta juyo ba ta ce " calm down , ni ba da niyar fada na kira ka ba " ta fada da larabci Ya na shirin daukar takobi ta fadi hakan Ya na jin abun da ta fada ya juya ya fara takawa ya karaso geffen ta ya tsaya ya nade hanayan shi a kirji ya na kallon cikin Window din shi ma Sai da su ka dauki lokaci a hakan kafin ta juyo slowly ta kale shi Kyakyawar budurwa ce mai jini a jika , ta so ta dan yi kama da NAWFEL , amma kuma kama ta jini , sannan launin idanun ta hazel ne kamar na shi bayan haka ba abun da ya yi kama tsakanin su , a shekaru za ta kai 27 haka ina kyautata zaton wannan ita ce RIANNA BIN JAABAR Cikin sanyi murya ta ce " Amir , wai me ya ke damun ka ? " Girgiza mata kai ya yi ba tare da ya kale ta ba allamun ba komai Hannu ta kai ta shako wuyan shi ta kai mishi bugu a ciki , ta na fadin " Wa za ka yiwa miskilanci , kar ka manta na girme ka fa " " Please Ukhtie let me " ya fada cikin siririyar murya Sakin shi ta yi kafin ta sa hannu ta tura shi kadan har ya yi baya zai fadi Cikin zafin nama ya taro kan shi ya mike tsaye ya na kallon ta Nade hanayan ta ta yi a kirji ta na kallon shi ta ce " za ka fada min ko sai na karaya ma ka hannu " ta kai karshen ta na daga mishi gera guda Ajiyar zuciya ya sauke , kafin ya ce " wlh ki na son takura min dayawa ni na fada miki ba abun da ke damu na " Ya kai karshen ya juya , ya fara takawa ya na neman ya bar wajen Da sauri ta sa kafa ta tade shi , ya fadi dib ga kassa A hankali ya dago ya mike zaune ya na kallon ta ya shagwabe fuska kamar karamin yaro ya ce " wai me na yi miki da za ki dake ni haka in da kin ji min ciwo wlh sai na fadawa Abbi " Yar karamar dariya Ta yi kafin ta zaune kassa ita ma ta na kallon shi ta ce " ban son shirme AMIR wa za ka yi wa shagwaba , ko kunya ta ba ka ji , ni yanzu fada min , mi ke damun little brother di na " ta kai karshen cikin zolaya Kauda kai gefe ya yi ya na dan turo karamin bakin nan nashi ya ce " ni kyale ni ba abun da ke damu na " Dariya sosai ta yi , ta na kallon shi ta ma rasa abun da za ta ce mishi [16/09 à 09:57] M.N.M: ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) ⚘🕊 MALLAKIN MEERAH 🕊⚘ 【 CUTIE PIE 】 Marubuciyar littafin :【 TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 】 YOU CAN FOLLOW MY WHATSAPP CHANEL 👇👇👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK .............. 2 🌹👑 【 THE ROYALTY LOVE ✌👑🌹】 ________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊________________ P A G E 2 ❤ 🔥 Dawo kallon shi ya yi kan ta ya na matse gera ya ce " ki bar min wannan dariyar ta ki ta keta " Tsagaita dariyar ta ta yi kafin ta ce " okay , okay , Akhie fada min me ya ke damun ka " Sai da ya dan jinkirta kafin ya ce " Ukhtie , Abbi ya ce gobe zan fara bin shi fada , dan in ga yadda ke kula da masarauta " " okay , minene matsalar to , ko ba ka son zuwa " ta tambayeshi " ni fa na fada mishi ba ni son zama MALIK bayan shi amma ya ki sauraro na " ya fada cikin sanyi Daura hannun ta ta yi saman kafadar shi ta ce " in tambaye ka , in ba ka hau mulkin Saudiya ba , me za ka yi , kai kadai ne fa yarima cikin ahalin mu " Dan turo baki ya yi cikin shagwaba ya ce mata " ni na fada mishi company Sarrafa petroleum na ke son budewa , kar ki manta ko a school business na ke karantawa , amma ya na neman ya daura min abun da ya fi karfi na , ni gaskiya ba zan iya mulkar mutane ba " Yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " gaskia kam ba za ka iya ba , da wannan shagwabar za ka zama Malik , ko Tesnim ba za ta gwada ma ka shagwaba ba " Hararrar wassa ya wurga mata ya na shirin magana ta mike tsaye ta mika mishi hannu ta na fadin " let's go see Abbi mu yi mishi magana a tare " Da sauri ya mika matta hannu ya mike tsaye ya na murmushi Ya na mikewa ya ji kamar karar faduwar karfe a wajen kofar shigowa wajen A tare su ka kai duban su a wajen kafin Amir ya fara takawa a hankali ya nufi wajen da ya jiyo karar Cikin nitsuwa Ta tsayar da shi da cewa " ina kuma za ka je ka bar alkyabar ka " ta fada ta na fara takawa ta nufi table din ta dauki alkyabar sannan ta nufo shi ta ce mu tafi ko Ba musu ya bi bayan ta su ka bar wajen a tare ta na rike da Alkyabar shi Su na barin daya da ga cikin dakarun da ke tsaron wajen ya juya ya bar wajen da sauri sauri Sai da ya karaso kassan wata katuwar bishiya cen bayan masarautar inda babu kowa ko me wucewa babu sannan ya tsaya ya Zube saman guyiwowin shi ya na sunkuyar da kai ya ce " gaisuwa na ke ya shugaba na " Wani mutun ne zaune kassan bishiyar ya na sanye da wasu kaya bakake Dukan su , Idanun shi kadai a ke iya gani saboda ya rufe fuskar shi da wani bakin harami baki shi ma Cikin wata murya cike da isa ya ce " ya a ke ciki ne ? " Ba tare da ya dago kan shi ba ya ce " ya shugaba na , na jiyo Amir na fadin zai fara shiga Fada tare da Malik " Da sauri mutuman ne ya katse shi da cewa " sai in ya na raye zai shiga Fadar " " Haka ne shugaba na " " gobe ina son in ji labarin mutuwar Amir , idan kuma ta wuce gobe kai za ka mutu a madadin shi Meli " Murya na kerma Meli ya ce mishi " in sha Allah ba za a samu matsala ba shugaba na , duk wani shirye shirye da za a yi mun yi shi , lokaci kawai mu ke jira " Jinjina kan shi mutuman ya yi kafin ya ce " ina jiran albishir mai dadi Meli , ni kuma zan cika maka alkawarin ka " " Godiya na ke ya shugaba na , Allah ya ja zamanin ka , Allah ya kare gaba da bayan ka ya shugaba na " Daga mishi hannu mutumin nan ya yi kafin ya ce " ya isa haka tashi koma bakin aikin ka " " godiya na ke ya shugaba na " Meli ya fada kafin ya mike kai a sunkuye ya bar wajen Ya na barin wajen mutumin nan ya bushe da wata shegiyar dariya ya na fadin " sai dai ka yi hakuri dan uwa na amma dole Mulkin saudiya ya dawo cikin tafin hannu na , ko da kuwa Malik din da kan shi zan kashe " ya kai karshen ya na sake bushewa da dariya kafin ya bace bat a wajen * MISALIN KARFE 8 NA DARE Wani katuwar dining room dauke da wata kyawatatar dining table Fara kal dauke da wasu chair goma sha biyu suma farare kal gwanin burgewa Table din shake ta ke da abincin kala kala da Fruits wannan abincin sai ya ciyar da gida je goma su ci su koshi har su samu na breakfast Nan na hango mutanan gidan zaune saman chair su shidda ne mata hudu da namiji biyu AMIR NAWFEL da wani dattijon wanda na san Shi ne MALIK din dan kamanin shi daya sak da AMIR NAWFEL har Hazel eyes din su MALIK ya na zaune saman chair din da ke tsakiya , geffen shi na dama RIANNA ce zaune tare da MALIKAT INAS sak kamanin ta da RIANNA Geffen hagun shi kuma AMIR NAWFEL ne zaune tare da TESNIM , sai MALIKAT AL'UMU ta so ta dan yi kama da AMIR NAWFEL amma ba sosai ba A hankali MALIK ya dago kai ya kali AMIR NAWFEL da ya sunkuyar da kai ya na cin abincin shi , amma da ga gani ka san ba dan ya na son abincin ba ya ke cin shi Dan karamin murmushi MALIK ya yi kafin ya kali yarinyar da ke zaune geffen shi ya ce " TESNIM yaushe za ki tafi Daular Ottoman , mun yi waya da kakan na ki ya ce ya shirya miki wata tsaraba ta musaman " Kunbure fuska TESNIM ta yi ta turo dan bakin nan nata gaba ta ce " Abbi ba AMIR ne ba na ce mishi yaushe za mu tafi ya ce wai shi ba zai je ba " Slowly AMIR ya dago kai ya kali TESNIM murya kassa kassa ya ce " dole sai da ni za ki je , ba ki san hanya ba ne " " NAWFEL laifin me ta yi maka da ga ta ce ka raka ta " MALIK ya fada ya na kallon AMIR Dan karamin tsaki ya yi kafin ya mike tsaye ya juyo ya fara takawa cike da nitsuwa ya bar wajen " NAWFEL ina za ka je ba ka Kamala abincin ka ba " RIANNA ta fada Ko amsa mata bai yi ba ya ci gaba da tafiyar shi Sai da ya bar wajen sannan ta juyo ta kali MALIK ta ce " Abbi don Allah ku janye maganar nan ta AMIR ya hau mulki wlh ba ya so " Daga mata hannu MALIK ya yi ya katse ta kafin ya ce mata " RIANNA ke da NAWFEL na ga bakin ku daya , idan bai hau mulki baya na ba wa zai hawa , ku nai sheda shi kadai ne yarima da na mallaka , ya tafi ya hura miki kunne ko , ya zuba miki shagwabar da ya saba ko " Marairaice fuska RIANNA ta yi ta na fadin " please Daddy , ku ba shi damar ya zabi abun da ya ke son yi , kar ku condemend din shi saman abun da bai da ra a yi , wlh Abbi tun da ya nuna ba ya son Mulkin nan wlh ko ya hau ba zai tsaya ya kula da saudiya kamar yadda ku ke yi " " RIANNA tashi fice min da ga gani sai ki bi bayan shi dama ke ce ke darme mishi gindi ya na abun da ya ga dama , to sai ki je ki rarrashe shi , ki kuma fada mishi gobe ya shirya bi na Fada " " Abbi ......... " Da sauri Malik ya daga mata hannu ba tare da ya ce komai ba Tashi ta yi ta na dan kananan magaganun ta bi bayan AMIR ita ma ta bar wajen Su dai Malikat kallon shi kawai su ke dan sun san halin Malik idan ya yanke shawara to babu wanda ya isa ya sa shi ya sauya shawarar nan dama haka nan ya ke da magana guda a ka san shi , duk irin halin da zai tsinci kan shi , shawarar kan shi kawai ya ke dauka , bai taba neman shawarar wani ba , Idan kuma abu ya shige mishi duhu shawarar Matan shi kawai ya ke nema Bayan RIANNA ta baro dining room din su kai tsaye wani kyawatencen parlour ta nufa nan ta isko AMIR zaune saman chair din Malik ta gold zalla ya daura kafa daya bisa daya ya kurawa Tv ido Dan zaro idanu RIANNA ta yi ta na kallon shi da sauri ta nufe shi ta na fadin " kai AMIR kujerar Malik za ka hau haka , maza sauka tun bai gan ka ba , ka fi kowa sanin bayan shi babu wanda ya isa ya hau wannan kujerar " Slowly AMIR ya juyo da kan shi ya kali RIANNA ya na dan lumshe idanun shi kamar mai jin barci , cike da izza ya ce mata " da ga yau ta zama tawa " ya kai karshen ya na meda kallon shi kan Tv Dan zaro idanu RIANNA ta yi ta na kallon shi baki sake , tun da ta ke da AMIR ba ta taba ganin ya yi mata kwarjini kamar na yau ba Ta na shirin magana ta jiyo Muryar Malik a bayan ta ya na fadin " yanzu sai ka tashi me ita ya zo " Dum ta ji gaban ta ya buga da sauri ta juya ta na kallon shi ta na dan zazzaro idanu Shi dai AMIR ko motsi bai yi ba asali ma ko kallon inda Malik ya ke bai yi ba ya ci gaba da kallon Tv ................... ( ku tsaya na dubo abun da ke cikin Tv din nan gaskia ) Ba komai ba ne face masarautar ya ke kallo ta cikin kananan camera da a ka boye ta ko ina cikin masarautar , shi dai kawai ya na kallon abun da ke faruwa a cikin masarautar ne amma hankalin shi na nesa Har sai da Malik ya karaso gaban shi ya tsaya ya na yi mishi magana bai sani ba Kawai sai ji ya yi an buge mishi kafar shi ta sama ta fadi kassa , Slowly ya lumshe idanun shi kafin ya bude su ya na kallon Malik ido cikin ido kafin ya ce " What ? " a takaice Ba Malik kadai ba har RIANNA da ke tsaye a bayan shi sai da ta zaro idanu ta na kallon AMIR " NAWFEL sauka da ga saman kujera ta " Malik ya fada cikin nuna isa Shiru AMIR ya yi na dan mintina kafin ya meda kallon shi kan Tv din ba tare da ya ce komai ba " Akhie ............ " Kut maganar ta yanke sakamakon daga mata hannu da Malik ya yi " Idan ka na son zama saman wannan kujerar , dole sai ka yarda ka amshi sunan ka na yarima mai jiran gado ka fara bi na Fada domin ganin yadda a ke kula da masarautar nan sannan za ka iya zama saman wannan kujerar " Slowly AMIR ya mike tsaye ya fara takawa a hankali ya karaso gaban Malik ya tsaya ya na kallon shi cikin ido ya ce " kujera ce dai sai na hau ta , sannan ni ba zan je Fada ba , ba na bukatar shawarar kowa ba na kuma bukatar sannin yadda a ke kula da masarautar , duk ranar da a ka nada ni a matsayin Malik tsari na kadai zan bi dan haka ka daina min zancen wata fada ni babu inda zan je " ya na gama fadar haka ya juya ya koma saman kujerar nan ya zauna ya daura kafa daya saman daya ya ci gaba da kallon Tv din gaban shi Shi dai Malik sumar tsaye su ka yi shi da RIANNA Sai ya kare mishi kallo da kyau sannan ya ce ma RIANNA ta ba su waje Ba musu ta juya ta bar parlour dama part din Malik ne su ke ciki sai ta bar part din baki daya dama su Malikat su riga ta tafiya TESNIM kuma ta tafi yawon birididin da ta saba , ba ta wannan part ba ta wacen duk in da ta kama ta tafiya ta ke yi A hankali Malik ya nufi wata Sofa da ke daman kujerar da AMIR ke zaune a kai shi ma ya zauna ya na kallon AMIR Kamar ko ya san kallon shi ya ke yi ya ce mishi " lafiya ka na kallo na haka " Girgiza kan shi Malik ya yi ya na murmushi ya ce " Mulki ya na kama ka AMIR why kullum ka ke abu kamar mace , sai dan karan shagwaba , ko takobi sai da RIANNA ta matsa sannan ka fara koyo , da ba hakan ba yanzu ko makiyi ya zo maka ba za ka iya kare kan ka ba " Shiru AMIR ya yi bai ce mishi komai ba Dariya Malik ya yi kafin ya dauki wani pillow saman sofar ya tila wa AMIR da sauri AMIR ya kauce pillow din bai same shi ba Dan karamin murmushin geffen fuska ya yi ya ce " Abbi , ni fa fada ne da makami ba ya burge ni , na fi son fada da hannu " " hmmm , hakan ba shi ba ne mafita ba , ya kamata a ce duk wani makami a duniya ka iya fada da shi , ba ka san ta yadda makiyin ka zai zo maka ba , bare kai da ka ke cikin gidan sarauta " Cikin nitsuwa AMIR ya katse shi da cewa " Idan kuma makiyin ya zo maka ta baya ? " Shiru Malik ya yi ya rasa amsar da zai ba shi Jin ya yi shiru ya sa AMIR juyo da kan shi ya kali Malik Dan karamin murmushi ya saki kafin ya ce " ba ka san ta yadda makiyin ka zai zo maka ba , amma na san wani abu , duk mai sanin ganin bayan ka , ba zai soke ka ta gaba , dole ta bayan idon ka zai soke ka , saboda ya san ka fi karfin shi ta gaba " " wait ! Maganar me ka ke yi min haka " Malik ya fada dan shi bai san abun da AMIR ke fada ba Meda kallon shi AMIR ya yi kan Tv sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce " ba komai kawai ina nufin ka zama me tsare bayan ka a kodayaushe saboda ba ka san ta inda makiyin ka zai zo maka ba , Idan kan ce ka za kare gaban ka kadai , to ta bayan ka zai zowa , dan haka ka zama mai kare gaba da bayan ka , saboda ba ka san da wa ka ke tare da shi ba , Makiyin ka zai zo ma ka da sufar aboki , aboki kuma da sufar makiyi " Dariya sosai Malik ya yi kafin ya ce " shi ya sa ban yarda da kowa cikin masarautar nan , ko a fada ba shawarar kowa ba ke doka ba " " Duk da hakan , yanzu idan na tambaye ka cikin fadar nan wanda ke zaune da kai da zuciya daya za ka iya fido min su " Shiru Malik dan ba kariya ya fada ba " Shi ya sa na ce ka zama mai tsare gaba da bayan ka , ba ka san wanda ka ke tare da shi ba , ko da ya na zaune da kai da zuciya daya , wata rana zai iya juya maka baya " Dogon nunfashi Malik ya ja kafin ya ce " kai ni fa hirar nan ta ka mara ma'ana ta fara isa ta " Murmushi kadan AMIR ya yi kafin ya ce " ban rike ka ba tashi ka tafi " " ban son shirme , part di na ne ka ke ciki " Dariya AMIR ya yi ya na fadin " ba wajen matar ka ba za ka kwana , tashi ka je ni a nan zan kwana " " kai eh fa haka ne ka ma tuno min , bari na tashi na tafi wajen baby na " ya kai karshen ya na mikewa tsaye Da sauri AMIR ya taro shi ya na fadin " Wait, Abbi wa ka ke kira da baby " Hararrar wassa Malik ya yi mishi kafin ya ce " Mummyn ka mana " ya kai karshen ya na kashe mishi ido guda Dariya sosai AMIR ya yi har da dafe ciki idanun shi na kawo ruwa Shi ma dai Malik yar dariya ya yi kafin ya tako kusa da AMIR ya dan sunkuyar da kai Ya rage sautin Muryar shi kamar mai rada ya ce " Ka na ji na ko , ita fa mace yar shagwaba ce ka bar ganin dan ta haifi zankadeden saurayi kamar ka , kullum ta na son a dinga ririta ta , a na shagwaba ta kamar baby , dan ba ka da matar ne shi ya sa ba za ka gane ba " " ba ni ma son na gane " AMIR ya fada ya na yar dariya " hmmm AMIR ina guje maka ranar da so zai maka mugun kamu , wlh sai ka yi kuka " Dan matsowa AMIR ya yi kusa da face din Malik murya kassa kassa ya ce " Har yanzu ba a yi macen da za ta Mallaki zuciyar AL-AMIR NAWFEL BIN JAABAR d'a tilo ga MALIK HICHAM BIN JAABAR jikan MALIK ABDOUL LATIF BIN SAUD , Har yanzu ba ta shigo duniya ba " Jinjina kan shi Malik ya yi kafin ya ce " Gaskia ne kam , izza a jinin ka ta ke , amma ka sani , mace ce ta haife ka , kamar yadda ta haife ka haka zalika , za ta haifi wadda za ta malake zuciyar ka , duk wannan izzar da ka ke nuna wa sai ta zube a gaban ta , ka jira ka gani " " Abbi , dubi wuce ka tafi wajen babyn ka , ni kyale ni film zan kala " Yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya kai bakin shi ya sumbaci forehead din AMIR sannan ya ce " ai kai ma baby na , I love you " Dan murmushi AMIR ya yi kafin ya ce " I LOVE YOU dad " Jinjina mishi kai Malik ya yi kafin ya mike ya juya ya fara takawa Har ya yi nisa ya jiyo Muryar AMIR ya na fadin " ka yi min magana da Azim " Jinjina mishi kai kawai Malik ya yi ba tare da ya ce komai ba har ya ficewar shi ya bar AMIR shi kadai Bai yi five minutes da fita ba wani mutumin ya shigo parlourn ya na sallama Ya sha ruwan mamaki ganin AMIR zaune saman kujerar da Malik ke zama , a sanin shi bayan Malik ba wanda ya taba zama saman ta sai yau ga AMIR zaune sama Karasowa gaban AMIR ya yi ya Zube saman guyiwowin shi ya sunkuyar da kai ya na fadin " Allah ya ja zamanin yarima , dan sarki jikan Sarki , ina mika gaisuwa na ga Adalin shugaba na , Umarnin kadai na ke jira " Daga mishi hannu AMIR ya yi kafin ya ce " ya isa haka Azim wani aiki na ke son ka yi min , kuma zan so ya tsaya a tsakanin mu " " umarnin kadai na ke jira ya shugaba na , yadda ka so haka za a yi " " ina son ka je part di na , Bedroom na farko ba wanda na ke barci ciki ba , ka duba cikin bedside drawer , akwai passport di na , da Visa , duk ka dauko su , sannan ka shiga ka duba cikin closet , ka dauko jakar cumputer di ta ka saka su a ciki ka kawo min ina jiran ka " Da sauri Azim ya ce " An gama shugaba na " ya na gama fadar hakan ya tashi da sauri ya fice parlourn [16/09 à 09:57] M.N.M: ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) ⚘🕊 MALLAKIN MEERAH 🕊⚘ 【 THE ROYALTY LOVE ✌👑🌹】 Marubuciyar littafin :【 TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 】 YOU CAN FOLLOW MY WHATSAPP CHANEL 👇👇👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK .............. 2 🌹👑 ________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊________________ {PAGE 3 ❤🔥} Ya na fita AMIR ya mike tsaye ya nufi glass din da ke bayan shi dan duk ginin na glass ne Ya tsaya ya na kallon masarautar ya na nade hanayan shi a baya Ya dauki wajen good ten minutes a hakan kafin Azim ya dawo cikin parlourn ya na sallama Ba tare da ya juyo ba ya amsa mishi sannan shi cen kassa kassa Geffen shi Azim ya karaso ya Zube saman guyiwowin shi ya na fadin " An gama ya shugaba na , ga abun da ku ka bukata " " Ajiye saman Sofa ka zo ina son magana da kai " Ba musu Azim ya tashi ya koma cikin parlourn ya ajiye jakar saman sofa kafin ya komo geffen AMIR ya Zube saman guyiwowin shi Cikin nitsuwa AMIR ya ce mishi " mike tsaye Azim , ka san fa ka girme ni a shekaru " Mikewa tsaye Azim ya yi ya dan ja baya kadan ya tsaya ya na sunkuyar da kan shi sannan ya ce " ya shugaba na , tabass na girme ka da shekaru , amma ai matsayin ka sama da nawa ya ke " Dan karamin murmushi AMIR ya yi kafin ya ce " Azim duk wannan matsayin ba komai ba ne , a wajen Allah duk daya mu ke , zan tambaye ka wani abu Azim kuma ka fada min gaskia " " in sha Allah shugaba na idan na sani zan fada maka " Gyada kan shi kadan AMIR ya yi kafin ya ce " ina son ka fada min , a ganin ka zan iya yin mulkin saudiya kamar na Malik " Dan karamin murmushi Azim ya yi cikin girmamawa ya ce " Ba zan yi maka kariya ba Shugaba na " Da sauri AMIR ya katse shi da cewa "ka kira ni da suna na " Kara fadada murmushin shi Azim ya yi kafin ya ce " ba zan yi maka kariya AMIR amma ina ji a jiki na ba za ka yi mulki irin na Malik ba , no ! Na ka na musaman ne , da sabon salo zai zowa , na san za ka zama Adalin shugaba , Za ka yi Mulki kamar na MALIK AL SAUD dan mulkin shi har yanzu tarihi ne , ka na da zuciya mai kyau ya shugaba na , ina fatan za ka mulke mu da wannan kyakyawar zuciyar ta ka " Dan karamin murmushi AMIR ya yi kafin ya ce " yanzu a ce ba na nan " Da sauri Azim ya ce " ba na fatan hakan AMIR domin duk cikin yaran shi Malik ya fi kaunar ka , wannan kowa ya shaide shi cikin masarautar nan , na san ba zai iya jure rashin ka ba " Shiru AMIR ya yi na dan mintina kafin ya ce " na gode Azim za ka iya tafiya " Dan sunkuyar da kai Azim ya yi kafin ya ce " na gode ya shugaba na , Sai da Safe " ya fada kafin ya juya ya fice parlourn Sai da Amir ya dauki wajen good 30 minutes ya na kallon cikin masarautar , ya na kallon yadda jami'an tsaro ke kai kawo Kafin ya daga kafa slowly ya juyo ya nufi wannan bakar Jakar da Azim ya ajiye saman Sofa ya dauke ta kafin ya juya ya nufi wani corridor da ke fuskantar sofar Sai da ya wuce kofa uku sannan ya iso ta hudun ya daura yatsar shi saman finger print Nan take kofar ta bude kan ta har da fadin sunnan shi A hankali ya shiga cikin dakin yanzu na sallama kassa kassa Wani tanpasheshen bedroom ne da ga gani ka san na Malik din ne da kan shi dan dakin ya kai girman parlourn da ya fito bai tsaya wani dube dube ba ya nufi bedside drawer da ke cen da ga cikin dakin Ya zauna bakin gadon , ya kai hannu ya bude box na farko Nan ya ga bandir bandir din kudi dirham shakke a wajen Jakar hannun shi ya bude ya sa hannu ya fara jidar kudin nan ya na saka wa a cikin jakar nan Sai da ya debi rabin kudin sannan ya meda box din ya bude na kassa Nan wajen kuma bandir din Dollar ne , cike a wajen Nan ma sai da ya debi wajen rabin kudin ya saka a cikin yar jakar nan sannan ya hakura ya meda box din ya like , jakar har ta yi yauni ta cika kamar za ta fashe Rufe zip din jakar ya yi sannan ya ajiye ta geffen shi kafin ya tashi ya nufi wata door Ya na isa ta bude kan ta ya shiga ciki Ya na shiga kofar ta meda ta kan ta After some minutes ya fito daure da towel a kugunshi allamun wanka ya yi Ya na fitowa ya nufi wata door ita ma dan nesa kadan da ta toilet Ya na isa wannan karan ma ta bude kan ta Bai yi five minutes ba ya fito sanye da wasu kayan barcin farare kal ma su mugun kyau kamar yanzu a ka ciro su da ga cikin leda , ya saki wannan lalawsan Darck black smooth hair din na shi ya zubo mishi har saman shoulder , sai tashin fitinannan kamshi ya ke ( kaiiiii , kudi duniya ne gaskia 🤣 amma na halak 🤣🤣🤣 ) Kai tsaye wannan royal bed ya nufa ya Haye ya konta ya lumshe idanun shi ya na karanto adu'ar barci Ba jimawa barci ya yi gaba da shi * MISALIN KARFE 2 NA DARE Ya na tsaka da barcin shi a hankali ya fara jiyo kamar warin kuna A dubu dari ya ware idanun shi , nan ya ga uban hayakin da ke tashi cikin bedroom din nan take ya fara tari ya na toshe hancin shi idanun shi su ka koma jazir Kafin ya yi yunkurin tashi duk hayaki ya gawraye dakin ba ka iya ganin komai Amma a hakan ya mike ya laluba jakar shi , ya rataya ta , sannan ya sauko da ga saman gadon ya na uban tari dan hayakin ya fara yi mishi yawa ya nufi dressing room ya shigo Kamar wutar jira ta ke ko , ya na shiga kofar shigowa dakin ta ba da wata razananiyar kara kamar ta watsewar glass , ta fadi kassa , finger print din kuma ya watse nan take wuta ta gawraye bedroom din komai sai da ya kone a ciki ( bari dai mu ga da ga wajen kuma ) Duk mutanan masarautar su na tsaye gaban Building din , dan wajen hawa uku gare shi Duk hawa ukun sun kama da wuta wajen ya koma jazir Azim da wasu mutanan biyu su na rike da Malik sai kiran sunan AMIR ya ke ya na a bar shi ya ceci ran yaron shi kar ya mutu MALIKAT AL'UMU ma haka zalika sai da MALIKAT INAS da MALIKAT DJAOUDATT da MALIKAT HOUDA su ka ririke ta TESNIM da RIANNA kuma sai kuka su ke yi , su na kiran sunan AMIR Su na a haka RIANNA ta saki wata razananiyar kara da ga haka ta dauke ta fadi a kassa sumamiya Da karfi MALIKAT INAS ta kira sunan ta , ta saki MALIKAT AL'UMU ta nufi diyar ta , ta na kiran sunan ta Ganin abun da ke faruwa ya sa Malik Zubewa kassa saman guyiwowin shi ya dafe kan shi da hannu guda ya na fadin " wai me ya ke shirin faruwa ne haka , Azim me ku ke jira har yanzu ba ku kashe wutar nan ba " Bai gama rufe bakin shi ba duk glass din ginin su ka tarwatse su na bada wani razanannan sauti su ka fado musu kassa da sauri kowa ya juyo bayan shi wasu har guduwa su ke Dan zaro idanu ta MALIKAT AL'UMU ta yi ta fadi sunan AMIR da karfi har Muryar ta na sarkewa , ta na gama fadar hakan ta dauke lokaci guda ta na neman zubewa da sauri MALIKAT DJAOUDATT da MALIKAT HOUDA su ka taro ta a tare Da sauri Malik ya mike tsaye ya na fadin " ku kawo min ruwa tun da ku ba za ku iya kashe wutar nan ba , AMIR di na ya na ciki , NAWFEL ka na ji na , kar ka ji tsoro yanzu na zo na fitar da kai " ya kai karshen hawaye na zubo mishi ya nufi ginin da gudu ya na taka glass din da ya zube a wajen duk kafafun shi su ka fashe Da gudu Azim da wasu dogarai su ka bi bayan shi su ka taro shi Azim na fadin " ku yi hakuri yanzu fireman sun iso , su na kan hanya , kar mu rasa ku duka " Ina Malik ko jin su ba ya yi sai neman kwatar kan shi ya ke Lokaci guda ya tsaya ya kai hannu ya dafe saitin zuciyar shi Da sauri Azim ya shiga kiran sunan Malik ya na tambayar lafia Kafin ya yi wani yunkuri Malik ya dauke kamar wutar nepa ya fadi kassa cikin wannan uban glass har sai da hannayan shi su ka farfashe su ka fara zubar da jini Cikin fitar hayaci MALIKAT INAS ta shiga fadin " inallillahi wa ina illaihi raji'un , ya Allah me ya ke shirin faruwa ne haka , Ga MALIKAT AL'UMU , MALIK , RIANNA duk a konce , AMIR din mu kuma na cikin wannan uban wutar , wai me ku ke jira ba ku kira firemen da ambulance ba , jira ku ke sai kowa ya mutu ne " Ta na gama rufe bakin ta Motoci goma na yan kwana kwana su ka shigo masarautar da mugun gudu su ka nufi building din nan su ka fara kashe wutar Su Malik kuma A ka dauko wata motar a ka dauke su da ga wajen a ka nufi word room din da ke cikin masarautar dan ba su agajin gagawa Duk wannan abun da ya faru a kan idon AMIR ya na kallon su dan tun lokacin da ya shiga dressing room ya fito building din ta hanyar sirri , ko shi Malik dan ya na cikin halin ha ula'i ne ya sa ya mance da hanyar , da zai iya shiga building din ba tare da wuta ta taba shi ba Duk wannan uban kiran da su ke yi mishi ya na jin su , kuma ya kallon su Lokacin da RIANNA ta fadi sai da ya kira sunan ta a hankali ya mika hannun shi nan take wasu hawaye su ka zubo mishi , cikin zuciyar ya na fara nadamar shawarar da ya yanke amma ba zai iya ja da baya ba Haka ya ci gaba da kallon su , su na kuka ya na kuka hawaye bibiyu kamar karamin yaro Har lokacin da ya ga Malik ya Zube kassa sannan ya yi sauri ya toshe bakin shi ya bar wajen da gudu ya fice masarautar ba tare da kowa ya gan shi ba Sai ga shi a saman wata doguwar hanya babu kowa a saman hanyar , Titi ya na da kyau sosai an raba shi biyu da wasu ciyayi sa ga tsakiya da flowers multicolore kamar rainbow Ga wasu manyan lamps zagaye da titin su na ba da haske sai ka ce da safe ne Hanyar doguwar ce babu kwana ko guda. Sai shaguna sa su ke gefe da gefen titin Haka ya kama hanyar nan da uban gudu , kamar zai tashi sama , ko takalmi babu a kafafun shi , duk taku daya in ya yi sai kassar ta ba da sauti dib dib gashin shi duk ya watsar mishi a jiki Gudu ya ke kamar babu gobe , kamar wanda a ka biyo a na son kashe shi Duk gudun nan da ya ke yi ya na rike da wannan jakar ta shi da hannu bibiyu Ya dauki wajen good ten minutes ya na wannan uban gudun kafin ya fara hango wani plaza Ya na isowa wajen plaza din nan wajen tsalaka titi ya rage gudun shi ya tsaya ya na meda nunfashi har da rike guyiwowin shi Sai da ya dai'daita nunfashin shi sannan ya dago Ya na shirin barin wajen da gudu ya ga wata dankareriar mota baka kirin ta sha gaban shi ta tare mishi hanya Dum ya ji gaban shi ya fadi , ya kassa motsawa sai bin motar ya ke da ido zuciyar shi na duka uku uku Ya na a haka ya ga an bude Side din driver an sauko da kafa guda cikin wasu sneakers farare kal kafin a ida sauko da gudar wani kyakyawan saurayi sanye cikin Suit farare kal shekarun shi sun zo daya da na AMIR Karewa AMIR kallo ya yi da kyau kafin ya ce " AL-AMIR NAWFEL ? what are you doing here in this time , mu je na meda ka masarauta " Wasu yawu AMIR ya hadiye kafin ya ce mishi " kai ina za ka je ? " Dan karamin murmushi ya yi kafin ya ce " I'm sorry my Prince , kassar ne zan bari yanzu haka airport zan je " Ajiyar zuciya AMIR ya sauke kafin ya nufi motar nan ya na fadin " ni ma garin zan bari mu je " ya kai karshen ya na bude kofar Side din me zaman banza ya shiga ya zauna Da sauri saurayin nan ya shiga Wajen Driver ba tare da ya tada motar ba ya ce " ka yi hakuri ran ka shi dade , amma ba za ka iya bi na ba " Wani mugun kallo AMIR ya wurga mishi sai da saurayin nan ya sha jinin jikin shi " let's go , ba tambayar ka na ke ba umarni ne " AMIR ya fada cike da izza Wasu yawu Saurayin nan ya hadiye kafin ya tada motar shi ya kama hanyar airport da gudu Sai da su ka yi tafiya mai dan nisa kafin AMIR ya juyo ya kali saurayin nan Dum ya ji gaban shi ya fadi lokacin da idanun shi su ka yi mishi arba da wani zanen sword guda biyu Da wani Lion a tsakiyar su ya bude baki hakoran nan na shi sun fito , a wuyan saurayin nan Cikin nitsuwa ya ce mishi " What is your name ? " ya tambaye shi Dan karamin murmushi saurayin nan ya yi kafin ya ce " ran ka shi dade suna na DIYA BIN ABDOUL MUJEEB ........ " Katse shi AMIR ya yi da fadin " Da ga Daular Ottoman ! " Hannu Diya ya kai ya shafi zanen da ke wuyan shi kafin ya saki wani cool murmushi ya ce " Eh , da ga Daular Ottoman , ni ne yarima na uku ga SARKI AHMED BIN ABDOUL MUJEEB " " ka na da ruwa kishi na ke ji " AMIR ya fada mishi cikin nitsuwa Yar karamar dariya DIYA ya yi kafin ya ce " AMIR na ce maka da ga Daular Ottoman na ke , tambayar da za ta fito da ga bakin ka shi ne in ina da ruwa , a ka je kashe ka a ka turo ni kassan ka na da makiya dayawa a saudiya " " ku ta shafa , ko kashe ni ka zo yi , ko ma minene matsalar ka ce , ka na da ruwan ne ? " Girgiza mishi kai DIYA ya yi ya na fadin " ba ni da , ban fito da komai ba sai kaya na , shi ma wani uziri ne ya biyo da ni masarautar Saudia , da tun da ga cikin masarautar Ottoman zan shi ga jirgi na bar kassar nan " Jinjina kan shi AMIR ya yi bai ce mishi komai ba Sai da su ka iso airport din a haka kafin ya ce mishi " yanzu wace kassa za ka je ? " Sai da DIYA ya yi parking din motar shi a parking space sannan ya juyo ya kali AMIR ya ce " gaskia ban sani ba , duk inda duniya ta kai ni , ba zan maka karya ba ina son adventure , dalilin da ya sa ma baro Daular Ottoman " bude kofar shi AMIR ya yi kafin ya ce " shikenan tashi mu je " Da sauri DIYA ya ce mishi " ina kuma za mu je yi Ran ka shi dade " Juyo wa AMIR ya yi ya kali DIYA sannan ya ce "ka ce min ba ka san inda za ka je ba , ni ma ban san inda zan je ba , dan haka ka tashi mu tafi inda kaddara za ta kai mu , idan kuma ba za ka bi ni ba okay , sai wata rana in mun hadu " ya kai karshen ya na sauka da ga cikin motar Da sauri shi ma DIYA ya sauko ya bude gidan baya ya sauko da trolley din shi da wata jakar sannan ya rufe ya bi bayan AMIR da sauri Dai'dai lokacin da ya ke shiga cikin airport din DIYA na biye da bayan shi Ya yi sa'a ko wajen babu kowa sai wasu security guda hudu da ke tsaron wajen , su na ganin shi duka su ka daga hannu su na sara mishi Bai bi ta kan su ba ya nufi wajen sayan ticket Receptionist na ganin shi ta mike da sauri ta na gaishe shi Bai bi ta kan gaisuwar ta ba ya ce " akwai jirgin da zai tashi yanzu " Cikin girmamawa ta ce mishi " yes Sir , amma AFRICA-Nigeria ya nufa " " ba laifi shi za mu shiga " ya kai karshen ya na bude jakar shi ya ciro bandir din Dollar uku ya ajiye gaban ta Murya na kerma ta ce mishi " I'm sorry Sir , jirgin ya cika , sai dai ku jira gobe akwai wanda zai tashi karfe 5 na yamma " Matse gera AMIR ya yi ya wurga mata wannan mugun kallon na shi cike da izza ya ce mata " ko da saman kan pilot ne zan zauna , idan ki ka bari jirgin nan ya tashi babu ni a ciki , ki tabbatar gobe ba za ka ki dawo aikin nan ba , dan haka gwara ki dauki kudin nan ki ja bakin ki yi shiru ki ba mu ticket tun ina miki cikin ruwan sanyi , idan kuma ki ka bari rai na ya baci za ki ji karkashin kassa " Wasu yawu ta hadiye da karfi murya na kerma ta ce " i'm so......rry sir " Ta na gama fadar haka ta shiga shirya musu ticket Babu ko na gode AMIR ya dauki ticket din nan ya yi gaba abin shi Shi dai DIYA ya na biye da bayan shi ba ya da abun cewa karfin ikon AMIR ya fi na shi nesa ba kusa ba A haka su ka shiga cikin jirgin nan duk da a cike ya ke , bangaran Flight attendant , su ka zauna har sai da jirgin ya daga A karfe 3 dai'dai ya nufi Nigeria ba tare da sun san abun da ke jiran su a cen ba [16/09 à 09:57] M.N.M: ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) ⚘🕊 MALLAKIN MEERAH 🕊⚘ 【 THE ROYALTY LOVE ✌👑🌹】 Marubuciyar littafin :【 TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 】 BOOK .............. 2 🌹👑 ________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊________________ PAGE ________4 ❤🔥 * PRESENT DAY * ZAYD " bayan mun baro Saudiya mu ka shigo Nigeria , da farko a Abuja mu ka sauka , bayan mun yi wasu yan kwanaki , na saye wani company na sarrafa bakin oil da a ka saka a kasuwa , da ya ke su na jin turanci sai abun bai zo da matsala ba , bayan wasu watanni mu ka koma Kano da zama cikin wata yar karamar unguwa , amma duk mutanan wajen daya biyu ne ke jin Larabci da Turanci , hakan ko ba karamin dadi ya yi min don ko magana mutun ya yi min ba na gane wa sai na yi shiru na , da ga haka har su ke min daukar kurma , da makaho saboda yawwan saka glass da na ke dan boye idanu na , sannu sannu Har DIYA ya koyi haoussa ta zauna a harshen shi , ya koya min ni ma amma duk da hakan ba na yi wa kowa magana duk da a yanzu ina gane abun da su ke fada , a shekarar da mu ka dawo Kano ,Allah ya hada ni da wannan family inda su ka dauke mu kamar yan uwan su , ban san abun da ya sa wannan familyn ke kaunar mu haka dan har abincin dare su ke aiko mana idan kuma DIYA ba ya nan mai gidan da kan shi ya ke zowa ya gayace ni zuwa gidan shi dan na ci , a haka rayuwa ta ci gaba , amma har ga Allah kullum ina tunanin ku , ina kuma tunanin komawa gida , kawai lokacin ne sai yanzu ya zo " ya kai karshen ya na dago kai ya kali mutanan cikin dakin Kuka Ne ya kubce ma TESNIM ta sa hannayan ta biyu ta rungume shi ta na fadin " Akhie why za ka tafi ka barni , ka san irin kewar ka da na yi " Dan bubuga bayan ta ya yi ya na shirin magana Malik ya riga shi cewa " kenan part di na da a ka kona kai ka ba da umarnin hakan " Girgiza mishi kai Zayd ya yi kafin ya ce " no ba ni ba ne , a ranar bayan na baro dining room na tafi parlourn , na zaune saman sofa na jiyo Muryar Wasu da ga cikin masarautar su na fadin yadda za a yi su kona part din Malik , amma su tabbatar da AMIR na ciki , jin hakan ne ya sa na tashi na koma saman kujerar ka na zauna ina kallon duk wani abu da su ke yi , amma ban ga face din su ba saboda sun saka rawani , nan ne wata Idea ta zo min , na yi anfani da wannan damar dan na bar masarautar , Saboda pressure ta yi min yawwa , ba ni da yancin kai na a cikin masarautar nan , duk wani abu da na fada maka ina so ba ka saurare na , sai ka ce min wai dole sai na hau mulki , al'halin na fada maka ba ni so ba ni so " Ya kai karshen ya na kauda kai gefe , nan ya ga Inaya ta kure shi da idanu sai zubar da hawaye ta ke Nan take idanun su , su ka sarkafe cikin na juna Ya na a haka ya jiyo Muryar Malik na fadin " Ka yi hakuri AMIR , na san da na saurare ka da duk wannan abun bai faru ba " Cikin nitsuwa ya katse shi da cewa " no Dad , gwara hakan da ta faru ko ba komai na samu damar haduwa da wannan ahalin " Dan karamin murmushi Malik ya yi kafin ya ce " Shikenan yanzu sai ka tashi mu koma gida , mun ci gaba da kula da kai a cen " " no Dad , ka yi hakuri ba zan iya tafiya na bar Family na a nan " Malik na shirin magana MALIKAT AL'UMU ta daura hannun ta saman na shi Dawo da kallon shi ya yi gare ta Nan ta girgiza mishi kai kafin ta juya ta kali ZAYD ta ce " AMIR duk yadda ka ke so haka za a yi , amma nan da one hour za mu bar garin nan " Gyada mata kai ya yi kafin ya daga ya kali DIYA ya ce " to kai malam , sai ku koma gida kai da ABDOUL ou shirya mana kayan mu , ku taho da mama , sai mun hade a airport " Dan sunkuyar da kai DIYA ya yi cike da zolaya ya ce " an gama ya shugaba na " Dariya sosai MALIK da TESNIM su ka yi Sannan DIYA ya ce ma ABDOUL su tafi , ba musu ABDOUL ya bi shi su ka fice dakin Su na fita ita ma Inaya ta mike Slowly ta bar dakin Da sauri Nesrine ta tashi ta bi bayan ta dan ta ga allamun ba cikin hayacin ta ta ke ba Da kallo Zayd ya raka su har sai da su ka fita sannan ya raba jikin shi da na TESNIM ya mike a hankali ya fice shi ma Da kallo Malik ya raka shi har sai da ya fita sannan ya yi yar karamar dariya yi ce " MALIKAT ina ga ba a banza yaron ki ya ki tafiya ba , ya fada tarko ne " Cike da rudu TESNIM ta ce " Abbi wane irin tarko kuma " " na soyayya " ya fada a takaice Yar karamar dariya ta yi kafin ta ce mishi " haba Abbi, wannan babyn ? Ko ni fa na girme mata ba ma ita ba duka su biyu " " TESNIM ba ki san soyayya ba ne , ba ruwan ta da shekaru , amma za ki gane hakan duk ranar da ki ka fada soyayya ke ma " Dan tabe baki TESNIM ta yi ta na girgiza kan ta ba tare da ta ce komai ba Bangaran Inaya kuma , ta na fitowa ta zauna saman Waiting chair da ke bakin kofar dakin Ta na zama Nesrine ta karaso gaban ta ta tsaya ta na kiran sunan ta Kamar da ga sama ta jiyo Muryar Zayd ya na fadin " Cutie are you okay ? " Slowly ta dago kai ta kale shi , ya na tsaye geffen Nesrine Dan karamin murmushi ta saki kafin ta jinjina mishi kai, ta mayar ta sunkuyar da shi A hankali ya kira sunan Nesrine " na'am " ta fada ta na juyawa ta kale shi Da kai ya yi mata allamun ta koma cikin dakin , ba musu ta juya ta koma cikin dakin ta ba su waje Da kallo ya rakata har sai da ta shiga dakin sannan ya tako a hankali ya zauna saman chair din da ya ke geffen ta Cikin sanyin murya ya ce mata " cutie fada min me ya ke faruwa , ko yanzu kin daina so na ne tun da kin ji ko ni wanene ? " Murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta ce " soyayyar ka ta zama wani bangare na cikin zuciya ta , mutuwa ce kadai za ta iya fitar da shi , kawai dai na ji dalilin da ya sa ba za ka iya so na ba , ni ba ajin ka ba ce , sai dai na zama mai maka shara da wanke wanke , ka fi karfi na yaya Zayd , don Allah ka yi hakuri ka yi tafiyar ka , ka bar mu a nan , ko ba komai zan rage radadin soyayyar da ba zan taba samu ba " A hankali ya lumshe idanun shi ya bude su sannan ya ce mata " ba zan iya tafiya na bar ku a nan ba gaskiya , inda ma a ce malam na raye , amma ba ya nan , ban san irin abun da zai faru da ku bayan tafiya ta ba , ni fa ba shawara na ke ba ki ba umarni ne " Yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " nan fa ba masarautar ta ka ba ce , ba ka da ikon ba ni umarni " Cikin nitsuwa ya katse ta da cewa " amma ina iya ba ki umarni a matsayi na na mijin ki " Wani cool murmushi ta saki ta dago kai slowly ta kale shi ba tare da ta ce komai ba Sai da ta gaji da kallon shi sannan ta meda kan ta , ta sunkuyar A hankali ya dan sunkuyar da kai ya leko face din ta ya ce " Wannan murmushin kuma na meye , ko ba za ki bi mijin ki ba " Kauda kai gefe ta yi ta na ci gaba da murmushin ta wanda ita kadai ta san na minene Ta na haka kawai ta ji ya rungumota ya hada kan ta da kirjin shi cikin sanyin murya ya ce " na ji dadi da babu abun da ya same ki , ba ki san irin sanyin da na ji cikin zuciya ta lokacin da na bude ido na gan ki " Dan karamin murmushi ta saki ta na kara lafewa a jikin shi Sai da su ka dauki lokaci a haka kafin ya sake ya tashi ya ce su koma ciki Noke mishi kafada ta yi cikin shagwaba ta ce mishi " ni ba zan koma ba " A hankali ya koma saman chair din ya zauna ba tare da ya ce mata komai ba ya san bai wuce ta ce ta na jin kunyar Malik ba A haka su ka zauna a wajen ba wanda ya sake cewa uppan har sai da Diya da Abdoul su ka dawo su ka same su a nan A tare su ka saki wani kyawatencen murmushi kafin Diya ya ce " AMIR za mu iya tafiya ko sai ka ida hira da babyn ka ne " Dan karamin tsaki Zayd ya yi kafin ya mike tsaye ya fara takawa ya yi gaba Ya na barin wajen Diya ya kali Inaya ya ce " Gimbiya , tashi ku je " Jinjina mishi kai kawai ta yi kafin ta mike a hankali ta bi bayan shi , ta na fitowa ta hango shi tsaye wajen wata dankareriar mota fara kal , mama na ciki zaune ya na yi mata magana , Wajen su Inaya ta karaso , ta na tsayuwa wajen ya ce mata ta shiga motar Ba musu ta bude ta shiga motar , shi kuma ya juya ya nufi wata motar daban ya shiga Abdoul da Diya kuma su ka nufi cikin dakin , Diya ya ce wa Malik za su iya tafiya yanzu Ba musu duka su ka tashi su ka fito dakin su ka baro Hospital din , cikin wasu irin manyan motoci ma su nunfashi Inaya da Nesrine su ka shiga mota guda tare da mama TESNIM da MALIKAT su ka shiga mota guda Abdoul shi kuma tare da Diya Sannan Malik da AMIR su ka shiga mota guda su ka bar Hospital din Kai tsaye airport su ka nufa cikin konciyar hankali Su na isa ko ten minutes ba su yi ba jirgin su ya daga dama cikin private jet din su Malik su ka zo , to cikin shi kuma su ka bar Nigeria * AFTER SOME HOURS * SAUDI ARABIA Misalin karfe 9 na dare jirgin su ya sauka a kassar Saudiya Airport din cike ya ke da ga Sojoji da dogarai , duk mutanan wajen da idanun su su ka sauka kan AMIR sai da su ka sha jinin jikin su Shi kuma AMIR ko a jikin shi , ko kallo ba su ishe ba kai tsaye ya nufi wajen motocin da a ka tanada musu , kowa ya shiga su ka bar airport din da mugun gudu kamar za su tashi sama Cikin abun da bai fi ten minutes su ka iso Daular saudiya Ba su Inaya kadai ba , har shi AMIR sai da ya yi mamakin ganin irin gyaran da a ka yi wa Daular ta zamo mishi kamar sabuwa Har building din Malik da ya kone , an meda shi sabo amma wannan karan mai hawa hudu a ka yi ya ni ka farko kyawo da girma Kamar ko Malik ya san abun da ke cikin tunanin yaron na shi sai ya yi dan karamin murmushi ya ce ma driver din su ya kai su building din Building din tun da a ka gena shi har yanzu babu wanda ya taba shigar shi , dan musaman Malik ya sa a gena shi saboda AMIR na shi ne na musaman , shi kuma Malik a ka yi mishi wani part din daban Sai driver ya iso bakin kofar part din sannan ya yi parking din motar Da sauri dogarai da ke tsaron part din su ka karaso gaban motar su ka budewa Malik kofa Ashe AMIR ne ke zaune a bangaran su na ganin shi su ka yi baya da sauri su na karanto kalmar shahada Ya na fitowa ya tsaya ya na karewa building din kallo nan take abun da ya faru tsawan shekaru ya dawo mishi sabo Ya yi nisa cikin tunanin shi ya ji Malik ya dafa kafadar shi ya na fadin " mu shiga ko " Dawo da kallon shi AMIR ya yi kan Malik cikin nitsuwa ya ce mishi " ka sa a kai matan nan wajen MALIKAT INAS " ya na gama fadar hakan ya daga kafa ya na taku cike da izza ya shiga cikin ginin Ya na shiga Azim ya karaso wajen ya Zube saman guyiwowin shi ya na gaishe da Malik ya na yi mishi barka da zuwa Amsa mishi gaisuwar shi Malik ya yi kafin ya ce " akwai wasu mata da ke tare da mu , yaran ka sa a kai su wajen MALIKAT INAS , matar kuma a isa da ita wajen MALIKAT HOUDA " ya na gama fadar hakan ya shiga cikin building din shi ma Ba musu Azim ya mike dan cika umarnin Malik Abdoul da Diya kuma ba su ma shigo Daular saudiya ba , Kai tsaye Daular Ottoman su ka nufa Bayan AMIR ya shiga building din kai tsaye wajen lift ya nufa ya Haye hawa na uku Kai tsaye lift din da parlourn ya ke sada ka , ya na shigowa ya ji zuciyar shi ta buga da karfi Cak ya tsaya waje guda ya na karewa wajen kallo , ya na nan kamar yadda ya bar shi , duk kayan da a ka saka mishi sak irin na farko Ya na a haka ya ji Malik ya dafa kafadar shi A hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce " zan shiga wanka ba ni son kowa ya dame ni " ya na gama fadar haka ya nufi wani corridor da ke saman damar shi Da kallo Malik ya raka shi sai da ya ga ya shiga bedroom guda da ga na cikin corridor din sannan ya saki wani kyawatencen murmushi ya nufi sofa ya zauna Ya dauki wajen good 30 minutes a haka kawai ya ji kofar lift ta bude , RIANNA ta fito da ga ciki da gudu ta na hawaye ta nufi Malik ta Zube kassa kussan kafafun shi ta na kuka ta ce " Abbi wai AMIR ya dawo , tun dazu na ke ji cikin masarauta wai sun ga AMIR ya shigo nan , Abbi wai da gaske ne , AMIR di na ne ya dawo , Abbi ku fada min " Dan karamin murmushi ya yi ya na fadin " ya isa haka RIANNA kukan na minene kuma " Da sauri ta katse shi da cewa " don Allah Abbi ku fada min da gaske ne wai , Wlh zuciya ta zafi ta ke yi min ji na ke kamar zan mutu , Abbi ina son na ga yan uwa na , na yi kewar shi sosai Abbi kullum da shi na ke kwana da shi na ke tashi cikin zuciya ta why zai tafi ya bar ni Abbi ? " ta kai karshen ta na kontar da kan ta saman cinyar Malik ta na ci gaba da kukan ta A hankali Malik ya kai hannu ya na shafa kan ta ba tare da ya ce mata komai ba , sai dan karamin murmushi da ya saki ya san abun da ta ke ji cikin zuciyar ta , duk da ba mahaifiyar su guda ba , amma son da RIANNA ke yi wa Amir ko Tesnim da su ke uwa guda ba ta yi mishi shi Sai da su ka dauki wajen good ten minutes a haka kafin AMIR ya shigo parlourn ya na sanye cikin wasu kayan barcin farare kal masu mugun kyau sai tashin fitinannan kamshi yake yi , ya na tafe kai a sunkuye ya na latsa wayar shi Kai tsaye wajen wannan kujerar ta gold ta Malik ya nufa ya zauna ya daura kafa daya bisa daya ba tare da ya dago kai ba ya ce " Abbi , ka sa a kawo min Fruits wlh yunwa na ke ji kamar na yi sati ban ci komai ba " A dubu dari RIANNA ta ware idanun ta ta dago kai ta kali saitin da ta jiyo Muryar shi Ya na zaune ya yi zaman kasaita, sai da ta ji zuciyar ta ta buga Lips din ta har kerma su ke yi wajen bude baki ta ce " Akhie !" Slowly ya dago kan shi idanun shi ba su sauka ko ina ba sai saman ta Meyar da kan shi ya yi ya sunkuyar kafin ya ce " Ukhtie , please je ki kawo min wani abu na ci wlh yunwa na ke ji " Malik ne ya amsa mishi da cewa " NAWFEL ban son shirme RIANNA ba ta girme ka ba ita ce za ta kawo maka abinci " A hankali ya daga kan shi sannan ya ajiye wayar shi saman yar table da ke geffen Chair din sannan ya sauko da kafar shi kassa ya mike tsaye ya na fadin " ai na san hanya ku yi zaman ku " ya fada ya na fara takawa Da sauri RIANNA ta mike tsaye ta sha gaban shi baki sake ta ke kallon shi ta kassa magana Dan karamin murmushin geffen fuska ya yi mata kafin ya ce " Lafya kin tare min hanya tun da ba za ki je ba gusa min ni na tafi " Ita dai ta kassa wani kwakwaran motsi sai kallon shi ta ke yi Ganin hakan ya sa shi kauda kai gefe kadan ya kali Malik ya ce " sai da na ce maka kar a dame ni " Bai gama rufe bakin shi ba kofar lift ta bude MALIKAT INAS da MALIKAT HOUDA su ka fito a tare Cak kowa ce ta tsaya ta na zaro idanu ta na kallon AMIR Ya na ganin su ya saki wani dan siririn tsaki ya juya ya koma kan Chair din da ya taso ya zauna ya na kauda kai gefe Sai zaro idanu su ke su na kallon shi , duk sun kassa magana Sai cen MALIKAT INAS ta karaso wajen Malik ta zauna geffen shi ta na ci gaba da kallon AMIR baki sake nan take idanun ta su ka kawo ruwa Kamar ya ji a jikin shi ya na juyowa ta fara zubar da hawaye , ya san ta hawayen kusa su ke abu kadan sai ta ta yi kuka kamar karamar yarinya , shi ya sa ya ce a kai su Inaya wajen ta dan ya san duk cikin masarautar babu mai kirki irin nata Ya na ganin ta fara zubar da hawaye ya saki wani cool murmushi ya ce " Haba Ammie su hawayen na minene " Wani murmushi mai dan sauti ta yi ta na girgiza mishi allamun ba komai Shi ma murmushi ya yi mata kafin ya taso da ga saman chair din shi ya koma geffen ta ya zauna kassa ya kontar da kan shi saman cinyar ta ya ce " na yi kewar ki Ammie na " A hankali ta daga hannun ta har kerma ya ke yi ta daura saman kan shi Dan lumshe idanun ta ta yi kafin ta bude slowly ta na sauke ajiyar zuciya [16/09 à 09:57] M.N.M: ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) ⚘🕊 MALLAKIN MEERAH 🕊⚘ 【 THE ROYALTY LOVE ✌👑🌹】 Marubuciyar littafin :【 TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 】 BOOK .............. 2 🌹👑 ________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊________________ PAGE………………… 5 ❤🔥 A hankali RIANNA ta karaso wajen shi ita da MALIKAT HOUDA ta zauna saman sofa Ita kuma RIANNA ta zauna gaban shi Ta na shirin magana ya riga ta cewa " kar ki yi min magana , tun dazu na ce miki yunwa na ke ji amma kin share ni " Ba ta san lokacin da kuka ya kubce mata ba , ta fada jikin shi ta rungume shi Shi ma rungume ta ya yi tsam nan take idanun shi su ka kawo ruwa amma bai bari sun zubo ba Sai da ta gaji da kukan na ta sannan ta dago da ga jikin shi ta sa hannu ta na goge hawayen ta saki wani cool murmushi ta ce " na dauka ka tafi har abada " Da sauri MALIKAT HOUDA ta katse ta da cewa " da ma in an mutu a na dawowa " Cikin zolaya AMIR ya amsa mata da cewa " eh a na dawowa , na hadu da mijin ki a cen , har ya ce na gaishe ki " Duk mutanan wajen sai da su ka yi dariya jin abun da ya fada Cuke fuska AMIR ya yi ya ce mata " ke ni fa da gaske na ke yi miki , amma fa ki yi hakuri ya yi sabuwar amarya a cen wadda ta fi ki kyau " " ba na son shirme ni tsarar wassan ka ce " ta fada ta na tsuke gera Jinjina mata kai ya yi kafin ya ce " eh , ni na ma tafiya ta barci na ke ji , Please Ammie na , ku kula da yaran nan dayar ba ta da cikakiyar lafya " ya kai karshen ya na mikewa tsaye Da sauri MALIKAT INAS ta ce mishi " wai su wanene yaran nan " Juyo wa ya yi ya kale ta kafin ya ce " sirikan ki ne " ya kai karshen ya na kashe mata ido guda ya juya ya ci gaba da tafiyar shi ya koma bedroom din da ya fito da farko Da kallo duka su ka raka shi sai da ya shiga sannan Malik shi ma ya mike ya na fadin " ni ma zan shiga sai da safe " ya fada ya na nufar corridor shi ma ya shiga bedroom din da ke kusan ta AMIR " to sai ku tashi mu tafi " MALIKAT HOUDA ta fada ta na mikewa tsaye Su ma dai MALIKAT INAS da RIANNA mike wa tsaye su ka yi su ka fice part din kowa ce ta koma part din ta Kai tsaye ko wace part din ta ta koma , RIANNA kuma ta bi MALIKAT INAS part din ta Su na shiga su ka ga INAYA da NESRINE zazaune a kassa sun takure waje guda Dan karamin murmushi RIANNA ta yi kafin ta nufe su ta na sallama A tare su ka dago kai su na amsa mata sallamar ta kafin su sunkuyar da kai Zama ta yi gaban su ta na murmushi ta ce " ya sunan ku " ta fada da turanci A hankali kowace ta bude baki ta fadi sunan ta " Masha Allah , ku saki jikin ku , ku dauki tamkar yar uwar ku ta jini , saboda duk abun da Dan uwa na ya nuna ya na son shi , to ni ma ina son shi " Jinjina mata kai su ka yi a tare ba tare da sun ce komai ba Ta na gama rufe bakin ta wata matar ta shiga parlourn ta na rike da tray shake da abinci ta kawo gaban su Inaya ta ajiye kafin ta mike ta koma inda ta fito Ta na barin wajen MALIKAT INAS ta shigo parlourn ta na sallama Wajen su Inaya ta nufa ta zauna saman sofa ta ce " maza kun cinye ba na son ganin komai saman tray din nan " Su dai Inaya da Nesrine kai a sunkuye sun kassa cewa komai Dan sunkuyar da kai RIANNA ta yi ta na lekon face din su ta ce " ko kunya ta ku ke ji " A hankali Inaya ta girgiza mata kai ta na sakin wani marayan kuka ta na cewa " ku kai ni wajen yaya Zayd di na " Da sauri Nesrine ta rungume ta ta na fadin " ke yi wa mutane shiru ko kunya ba ki ji ba " Kallon MALIKAT INAS RIANNA ta yi cikin harshen larabci ta ce mata " Momy ina ga ita ce wadda AMIR ke cewa ba ta da lafya " Gyada mata kai MALIKAT INAS ta yi kafin ta sauko kassa saman carpet geffen Inaya ta daura hannun ta saman shoulder din ta ta na fadin " baby ya isa haka kin ji ko , bari da safe ina kai ki wajen AMIR kin ji ko " ta fada cikin sanyi Gyada mata kai Inaya ta yi ta na raba jikin ta da na Nesrine ta sa hannu ta na goge hawayen ta Murmushi kadan MALIKAT INAS ta yi kafin ta kai hannu ta dauki spoon ta fara ba ta abinci da kan ta Ba kunya ba tsoron Allah Inaya ta bude baki ta na karba kamar wata baby , Nesrine ma sai da RIANNA ta matsa sannan ta dauki spoon ta fara cin abincin , nan take ta zame ta na ci dama yunwa ta ke ji Ita dai RIANNA kallon su kawai ta ke ta na murmushi nan take ta ji son su ya shiga zuciyar ta Sai da su ka Kamala sannan MALIKAT INAS ta ce da RIANNA " je ki cewa Lamiya ta karbo musu kayan barci wajen TESNIM " " no , momy akwai kananan kaya waje na za su yi musu " RIANNA ta fada dan ta san halin TESNIM bayan AMIR ba wanda ta ke ba wa kayan ta " okay tashi mu je ki yi wanka ku sake kaya sai ku konta ku huta , gobe zan sa a kawo muku kayan saka wa " MALIKAT INAS ta fada ta na mike ta nufi wani corridor da ke fuskantar su ta shiga door ta karshe Ta na shiga RIANNA ta mike ita ma ta ce musu su tasso Ba musu su ka tashi su ka bi bayan ta , ta shiga da su bedroom na biyu ta ce su shiga su yi wanka yanzu ta kawo musu kayan sakawa Da to su ka amsa mata kafin su shiga cikin dakin ita kuma ta wuce na ta bedroom Su na shiga Nesrine ta yi saurin shiga toilet Ba ta yi five minutes da shiga ba RIANNA ta dawo rike da wasu kayan guda biyu ta ce su saka sai da safe da ga haka ta juya ta bar musu dakin Bayan Nesrine ta fito , ita ma Inaya ta shiga ta yi wanka kafin ta fito har Nesrine ta saka kayan ta , ta bi lafiyar gado har barci ya dauke ta Ita ma kayan ta saka ta Haye gadon ta konta ba jimawa barci ya yi gaba da ita * MELI Wani mutun ne sanye da bakaken kaya ya rufe fuskar shi ya sa hannu ya shake wuyan Meli sai zaro idanu ya ke yi " Ba ka ce min AMIR ya mutu ba tsawon shekara 6 , wannan wanene to " ya fada da dan karfi Murya na kerma Meli ke fadin " wlh ya shugaba na , ni da kai na kunnawa part din wuta kuma ina da tabbacin AMIR na ciki a lokacin ban san yadda a ka yi ya dawo ya shugaba na " A fusace wannan mutun ya yi wurgi da Meli geffe guda har sai da ya fadi kassa Da sauri ya riko wuyan shi ya na meda nunfashi kafin ya dago kai mutumin nan ya bace bat babu shi * WASHE GARI ( misalin karfe 10 na safe ) *AMIR Konce ya ke saman katafaren bed din shi , ya yi rub da ciki , da ga shi sai short A hankali ya fara jiyo a na yi mishi knocking , dan karamin tsaki ya ja kafin ya ware idanun shi a hankali ya na kallon door din kafin ya ba da izinin shigowa Turo kofar Malik ya yi ya na yi mishi sallama Da kallo AMIR ya raka shi ba tare da ya motsa ba har sai da Malik ya karaso bakin gadon Murmushi kadan Malik ya yi kafin ya ce " To sai ka tashi safiya ta yi " " Saboda shi ne ka zo min tun da safe " AMIR ya fada cikin wata zazzakar murya cike da nitsuwa Mika mishi wayar hannun shi Malik ya yi kafin ya ce " Amshi to , Ammien ka ce ke son yin magana da kai " A hankali ya dago hannun shi ya karbi wayar ya kai ta a kunne ya na sallama kafin ya ce " barka da safya Ammie " Ba ta amsa mishi sallamar shi ba ta ce " AMIR ka na ina , don Allah ka zo part di na yanzun nan " ta na gama fadar haka ta katse kiran Yanayin da ta yi maganar ba karamin tada mishi hankali ya yi ba A dubu dari ya mike zaune ya diro da ga saman gadon ya shiga dressing room da gudu Shi dai Malik ya na karbar wayar shi ya juya ya bar bedroom din dan a na jiran shi a fada Bai yi one minute ba ya fito sanye da wata jallabiya fara kal har kassa da sauri ya sa kafa ya fice bedroom din Har hada wa ya ke yi da gudu cikin zuciyar shi ya na rokon Allah ya sa ba wani abu ya samu Inaya da Nesrine ba A haka ya fito building din , duk dogarai da ke tsatsaye cikin masarautar idan ya yi arba da shi sai ya shiga karanto kalmar shahada saboda wasu ba su san da AMIR ya dawo ba ga shi kuma ya sanye da Farar jallabiya sai su ka yi tunanin ko fatalwar shi ce Bai bi ta kan su ba ya wuce kai tsaye part din MALIKAT INAS ya wuce na MALIKAT AL'UMU Ko sallama babu ya shigo parlourn ya na kwalla mata kira , nan ya ga Nesrine zaune saman sofa Ta na ganin shi ta mike tsaye ta na yi mishi barka da safya Gaban ta ya karaso cikin fitar hayaci ya na tambayar ta ina Inaya , da yatsa kawai ta nuna mishi corridor ba tare da ta ce komai ba Da sauri ya juya ya na shirin shiga corridor din har ya yi taku biyu ya tsaya cak ya na kallon ta baki sake A hankali ta ke takowa kai a sunkuye Ta na sanye cikin wata kyakyawar gown Pink colour mai mugun kyau ta sha ruwan stone da ga kassa Ta daura wata Alkyaba fara kal da ga sama , en yi mata zanen flower da zare mai launin gold amma ba ta saka hular ba , ta bar wannan lalawsan gashin kan na ta ya zubo mata gefe guda saman shoulder Ba ta wani yi make up kawai lips balm ne ta shafa sai tashin fitinannan qamshi ta ke , ba karamin kyau ta yi ba kamar ka sace ta ka gudu Duk sai ya ji ya tsargu da kallon ta ya kassa janye idanun shi da ga saman ta Har sai da ta karaso gaban shi ta tsaya , slowly ta dago kai ta kali cikin idanun shi sannan ta saki wani cool murmushi cikin shagwaba ta ce mishi " ina kwana yaya Zayd " Shi dai da ido kawai ya ke bin ta ya kassa wani kwakwaran motsi ko idanun shi ya kassa kiftawa Su a haka ya jiyo Muryar MALIKAT INAS ta na fadin " tun asubahi ta tashe mu da kuka wai a kai ta wajen yaya Zayd din ta " A hankali ya daga kan shi ya kali saitin da ya jiyo Muryar MALIKAT INAS Ta na tsaye ita da RIANNA sai murmushi su ke yi A hankali ya daga kai sama ya lumshe idanun shi ya ce " ya rahman " kassa kassa kafin ya juya ya nufi sofa ya zauna ya daura hannayan shi biyu sannan face din shi kafin ya janye ya dago kai ya kali MALIKAT INAS ya ce " kun san irin tsoron da ku ka ba ni ko wanka fa ban yi ba na fito kamar wani zarrare " Yar karamar dariya RIANNA ta yi kafin ta karaso geffen shi ta zauna ta dafa shoulder din shi cike da zolaya ta ce mishi " minene laifin mu dan Gimbiya na son ganin Yariman ta , mu taimaka mata kawai mu ka yi " A hankali ita ma MALIKAT INAS ta karaso ta zauna daya geffen na shi ta riko hannun shi ta ce " AMIR fada min gaskia me ke tsakanin ka da wannan yarinyar " ta fada da larabci dan kar Inaya ta ji abun da su ke fada Slowly ya dago kai ya kali Inaya da ke tsaye har yanzu ta sunkuyar da kai ta riko hannayan ta Sai da ya dauki dan lokaci ya na kallon ta kafin ya bude bakin shi a hankali ya ce " We are married " RIANNA ba ta san lokacin da ta saki wata yar siririyar kara sai da ta sa hannu ta toshe bakin ta Hararrar ta MALIKAT INAS ta yi kafin ta kali AMIR ta ce " Malik ya san da wannan zancen " " no , ina fada mishi yanzu idan na koma " ya fada ya na mikewa tsaye ya nufi hanyar fita Har ya kai bakin kofar ya jiyo Muryar Inaya ta na kiran shi Slowly ya dan juyo da kan shi ya na kallon ta ta geffen ido Cike da shagwaba ta ce mishi " yaya Zayd ka dawo amma ko " ta fada da haoussa Gyada mata kai kawai ya yi da ga haka ya juya ya bar wajen Dan karamin murmushi ta yi ta na sunkuyar da kai Bangaran AMIR kuma ya na fitowa ya ci karo da Azim Da sauri Azim ya Zube saman guyiwowin shi ya na fadin " gaisuwa na ke ya shugaba na , Allah karre mana yarima , dan sarki jikan sarki , duk mai taba ka mutuwa ce makomar shi " Cikin nitsuwa AMIR ya katse shi da cewa " ya isa haka Azim , me ke tafe da kai " " ya shugaba na , MALIKAT AL'UMU na son magana da kai " Takawa AMIR ya yi ya fara yin gaba , da sauri Azim ya mike ya bi bayan shi dan nesa kadan dan kar su zo dai'dai Sai da su ka dan yi nisa da part din MALIKAT INAS , ya wuce part din MALIKAT AL'UMU sannan ya ce ma Azim " ka shirya min zama da ita a garden ina zuwa " " an gama ya shugaba na " Azim ya fada ya na sunkuyar da kai kafin ya juya Shi kuma AMIR ya nufi Building din shi , kai tsaye hawa na uku ya nufa ya koma bedroom din shi , ya na shiga ya wuce toilet dan ya yi wanka After some minutes ya fito sanye da bathrobe , ya wuce dressing room Jim kadan ya fito sanye da trouser Navy blue , da Shirt white color , ya daura wata alkyaba fara kal da ga sama , duk da bai da gashi dayawa a yanzu sai da ya sa wata yar pin ya daure shi a baya sannan ya daura hular Alkyabar shi , sai tashin fitinannan kamshi yake yi A haka ya sa kafa ya fito bedroom din , kai tsaye part din ya fice baki daya Duk inda ya wuce sai ma su tsaro sun zube saman guyiwowin su , su na gaishe da shi Bai bi ta kan gaisuwar su ba ya nufi wani tanpasheshen garden Cike ya ke da ciyayi da flowers , sai wata yar hanya da za ta sada ka da wata katuwar runfa dauke da wasu lamusasun sofas farare kal guda hudu uku two seaters , daya kuma three seaters , geffen kowa ce sofa akwai wata yar karamar table ta glass , da ga tsakiyar su kuma an shinfida wani kyakyawan carpet Fari kal mai ratsin ruwan gold gwanin burgewa Duk wajen zagaye ya ke da dogarai , da guards rike da gun A haka ya karaso kassan runfar inda ya tardo MALIKAT AL'UMU zaune saman sofa three seaters , ga yar karamar table gaban ta dauke da wani tray shake da fruits A hankali ya motsa lips din shi ya na sallama , wadda shi kadai ya ji kayan shi Sannan ya nufi sofa two seaters ya zauna ya na fadin " Good morning momy " Daga mishi hannu ta yi ta na matse fuska ta ce " na yi fushi da kai " Cikin sanyin murya ya ce mata " Momy me kuma na yi ? " Hararrar wassa ta yi mishi kafin ta ce " where is My morning Hug ? " Maganar ta ta , ta so ta ba shi dariya ma amma sai ya danne kayan shi ya tasso a hankali ya koma geffen ta zauna sannan ya rungume ta Wani kyawatencen murmushi ta saki kafin ta ce " Na yi kewar sosai ka sani ko ? " Ya na shirin dagowa da jikin ta , kawai ya ji an fado mishi a baya Ko bai duba ba ya san ko wanene hakan ya sa shi cewa " tashi kar ki karaya min baya " A hankali ta tashi ta na yar karamar dariya ta ce " ina kwana Akhie " Raba jikin shi ya yi da na MALIKAT AL'UMU kafin ya tashi ya koma saman sofar da ya taso " Akhie wai su wanene yaran nan da ka taho da su ? " TESNIM ta tambayeshi ta na gyara zaman ta saman sofar Koma wa ya yi ya jingina bayan shi a jikin forehead din sofar ya daura kafa daya sama daya ya kale ta sannan ya ce " saman kan ki su ke ne ? " Ta na shirin magana Diya ya shiga wajen ya na sallama Abdoul na tare da shi Da sauri TESNIM ta mike tsaye ta na yar kara ta nufi wata yar budurwa da ke tsaye bayan Diya ta rungume ta ta na fadin " oyoyo , Rouksar , why ba ki fada min ba za ki zo " Yarinyar da ta kira da Rouksar fara ce kal a shekaru za ta kai 22 haka , ta na da kyau dai'dai gorgaudo , ta so ta yi kama da Diya , amma fa kama ta jini da ga gani ka san kanwar shi ce Rungume TESNIM ta yi ita ma ta na fadin " ni ma ban shirya tahowar ba , na ga Akhie ne zai tahowa shi ne na biyo shi dan na gan ki na yi kewar ki sosai my TESNIM " Da ga haka su ka raba jikin su Rouksar ta nufi MALIKAT AL'UMU ta rungume ta ta na fadin " Barka da wannan lokaci Momy " Dan bubuga bayan ta MALIKAT AL'UMU ta yi kafin su raba jikin su ta koma geffen ta ta zauna , TESNIM ita ma ta koma geffen ta ta zauna Diya da Abdoul kuma su ka nufi dayar sofa two seaters su ka zauna Abdoul dai tun da ya zo ya ke karewa AMIR kallo duk sai ya ga lokaci guda ya sauya mishi Da haoussa Diya ya yi wa AMIR magana ya ce " AMIR ina ????? " ya kai karshen ya na daga mishi gera guda A hankali AMIR ya juya kan shi ya kali TESNIM ya ce mata " TESNIM je ki kira min yaran nan " Tsuke fuska ta yi ta na kauda kai gefe wai ita ba za ta je ba " Idan ki ka bari na maimaita abun da na ce , jikin ki zai fada miki " ya fada cike da izza Da sauri ta mike tsaye ta na dan gunguni ta fara takawa ta bar wajen ta na tafe ta na kunbura fuska wai ita ta ji haushi Ta na barin wajen Rouksar ta saki wani kyawatencen murmushi ta na kallon AMIR ta ce " AMIR ba ka ganin ba ne tun dazu ka kyale ni " " ke Rouksar ban son shirme AMIR din ne ki ke jira ya fara gaishe ki " Diya ya fada cikin tsare gida Dan sunkuyar da kai ta yi ta na fadin " ka yi hakuri Akhie , ina kwana " ta fada cikin girmamawa Gyada mata kai kawai ya yi ba tare da ya ce mata komai ba Da ga haka ba wanda ya sake cewa komai har sai da TESNIM ta dawo tare da Inaya da Nesrine su ka shigo cikin runfar su na sallama Da sauri Inaya da Nesrine su ka nufi Abdoul su ka rungume shi su na yar dariya Rungume su shi ma ya yi ya na fadin " my sisters , da fatan na same ku lafya ? " Inaya ce ta riga Nesrine cewa " Lafya lau yaya Abdoul , ina ka tafi ka bar mu jiya tun bayan fitowar mu jirgi ban gan ka ba " ta kai karshen ta na raba jikin ta da na shi ta koma saman sofar da AMIR ke zaune ta zauna geffen shi Ita kuma Nesrine ta zauna kassa saman carpet geffen shi A tare TESNIM da Rouksar su ka zaro idanu su na kallon Inaya ta na zaune saman sofar da AMIR ke zaune kuma bai ce mata komai ba , ko ita TESNIM yanzu in a ka ce mata ta yi hakan ba za ta iya ba Ita dai MALIKAT AL'UMU ko a jikin ta sai ma tashi da ta yi ta bar wajen ta nufi part din ta Ta na barin wajen AMIR ya juyo da kan shi ya kali Inaya kassa kassa ya ce mata " kun yi breakfast ? " Juyowa ta yi ta kaleshi ita ma ta na murmushi ta gyada mishi kai " za ki sha fruits " ya tambaye ta Yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " no ni na koshi , sai dai in so ka ke ciki na fashe " ta fada cikin shagwaba Girgiza mata kai ya yi kafin ya kali Nesrine ya ce mata " Nesrine ina son yin magana da ke " ya kai karshen ya na mikewa ya fara takawa ya fice runfar Da sauri Nesrine ta tashi ta bi bayan shi Su na barin wajen Rouksar ta kali Inaya sama da kassa kafin ta kali Diya ta ce " Akhie su wanene wannan ?" Ta kai karshen ta yi wa Inaya kallon kaskanci Nuna ta da yan yatsa Diya ya yi kafin ya ce " saurare ni da kyau Rouksar na san abun da ya kawo ki masarautar nan , tun wuri ki sauke idanun ki da ga saman yarinyar nan , wlh ko gashin ta ki ka taba AMIR zai iya kashe ki , kuma ba abun da zai faru " Da sauri TESNIM ta katse shi da cewa " Dalilin mi Akhie zai kashe ta saboda wannan dan babyn ? " ta kai karshen ta na nuna Inaya da dan yatsa Yar karamar dariya Diya ya yi kafin ya ce " bari in ya dawo sai ki tambaye shi ai kun fi kusa " Duk maganar nan da su ke yi a kunnen Abdoul dan shi ya na jin larabci ba kamar Inaya ba , abun da bai sani ba ita ma ta na jin larabcin amma sama sama , duk maganar nan da su ka yi ta dan gane rabin ta amma sai ta nuna kamar ba ta ji su ba , sai da ta bari sun Kamala sannan ta tashi ta dauki Apple guda da ke saman table din gaban sofar su TESNIM sannan ta koma ta zauna ta na cin Apple din ta [16/09 à 09:57] M.N.M: ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) ⚘🕊 MALLAKIN MEERAH 🕊⚘ 【 THE ROYALTY LOVE ✌👑🌹】 Marubuciyar littafin :【 TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 】 YOU CAN FOLLOW MY WHATSAPP CHANEL 👇👇👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK .............. 2 🌹👑 ________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊________________ PAGE ……………………6 ❤🔥 Bangaran AMIR kuma , a tare su ka baro wajen shi da Nesrine su ka sauka da ga saman Hanyar ya shiga cikin ciyayin sannan ya tsaya ya rike hannayan shi a baya ita kuma ta na tsaye geffen shi Sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce mata " kin san dalilin da ya sa na kira ki ?" Girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " a'a yaya Zayd " A hankali ya dan lumshe idanun shi ya bude kafin ya dan juyo da kan shi ya kale ta ya ce " da farko ki daina kira na da yaya Zayd , ki kira ni da Akhie ko kuma AMIR " Da to ta amsa mishi Shiru ya yi na dan lokaci kafin ya ce " na san malam ya fada miki auren da ke tsakanin da Diya kafin ya rasu " Sunkuyar da kai ta yi kafin ta ce " Eh ya fada min , ranar da wadanan mutanan su ka zo gida su ka tafi da shi " Gyada kan shi ya yi a hankali kafin ya ce " ina fatan ba ki da matsala da hakan " Girgiza mishi kai ta yi allamun babu " okay , Gabe za ki bi shi masarautar su ya gabatar da ke ga Familyn shi , Idan kuma a nan ki ke son zama ba matsala za a ware muku part " Da sauri ta ce mishi " ni a nan zauna tare da Mama da Inaya , ba zan iya yin nesa da su ba " ta kai karshen kuka ya na kubce mata A hankali AMIR ya hannu ya janyo ta jikin shi ya rungume ta dan ya san ba komai ba ta ke yi wa kuka ba face malam , ko shi hakan ya ji cikin zuciyar shi da ya kira sunan shi amma ba yadda zai yi dole ya danne Sai da ya ji ta yi shiru sannan ya sake ta ya ja hannun ta su ka koma cikin runfar nan Ya na zuwa ya mikawa Diya hannun ta Murmushi Diya ya yi kafin ya riko hannun ta ya janyo ta ta zauna tsakiyar su shi da Abdoul ta na sunkuyar da kai Shi kuma ya koma geffen Inaya ya zauna , Ya na zama Azim ya karaso wajen ya Zube gaban AMIR ya na fadin " gaisuwa na ke ya shugaba na , mai martaba na son ganin ka a Fada yanzun nan " Shiru AMIR ya yi na dan mintina kafin ya ce " za ka iya tafiya " " godiya na ke ya shugaba na " ya na gama fadar haka ya tashi da sauri ya bar wajen Ya na barin wajen AMIR ya daga kan shi sama ya lumshe idanun shi " AMIR ba za ka je ba ne " Diya ya fada mishi dan ya ga allamun ba ya da niyar tashi Shiru AMIR ya yi bai ce mishi komai ba , bai kuma saukowa da kan shi ba Ya na a haka ya ji kawai an kontar da kai saman cinyar shi Slowly ya sauko da kan shi ya bude idanun shi , ya na kallon ta Allamun barci ta ke ji dan har ta lumshe idanun ta , ta daura kafafun ta saman Sofar Bai ce mata komai ba ya daga kan shi ya lumshe idanun shi " Rouksar tashi mu tafi ko ? " TESNIM ta fada ta na mikewa tsaye Karewa AMIR da Inaya kallo Rouksar ta yi kafin mike ta bi bayan TESNIM su ka bar wajen Su na barin wajen shi ma Abdoul ya mike ya na fadin " Diya ina mama ta ke ina son ganin ta " Cikin nitsuwa AMIR ya riga Diya cewa " ta na part din MALIKAT HOUDA " Gyada mishi kai Diya ya yi kafin ya mike ya riko hannun Nesrine ya ce su tafi Abdoul na biye da bayan su , su ka bar AMIR da Inaya a wajen sannu sannu har AMIR da Inaya su ka share wajen good on hours a haka ita ta yi barci shi kuma ya tafi duniyar tunanin shi , Allah kadai ya san abun da ya ke tunani ya na a haka kawai ya sake jiyo Muryar Azim ya na yi mishi sallama Dan karamin tsaki ya yi kafin ya sauko da kan shi , shii ya ma manta da cewa a na jiran shi a Fada gaishe shi Azim ya yi kamar yadda ya saba sannan ɗaura da cewa Malik na son ganin shi a part din shi "Okay " ya fada a takaice kafin ya sa hannu a hankali ya sauke kan Inaya da ga saman cinyar shi ya mike tsaye sannan ya juya ya dauke ta cak kamar baby ya juya ya fara takawa ya bar wajen Azim na biye da bayan shi dan wannan karan Malik ya ce kar ya dawo ba tare da AMIR ba shi kuma AMIR kai tsaye part din MALIKAT INAS ya wuce da Inaya da sallama cen kassan makoshi ya shigo parlourn MALIKAT INAS nan ya tardo ta zauna ita da RIANNA su na hirar su su na ganin shi dauke da Inaya su ka mike su ka nufe shi a rude su na tambayar me ya same ta bai bi ta kan su ba ya wuce ya kontar da ita saman Sofa sannan ya juyo ya kale su ya ce " barci ne ta ke yi " ya na gama fadar haka ya raba ta geffen su ya wuce ya fice part din wani cool murmushi RIANNA ta yi kafin ta tako ta zauna kusan Inaya ta ce " Ammie , ina ji a jiki na yarinyar nan she is so special for AMIR , duba ki yadda ya ke kula da ita kamar baby " ita ma MALIKAT INAS wani dan karamin murmushi ta yi kafin ta koma inda ta taso ta zauna ta na fadin " dole ya kula da ita saboda ya na son ta , zalar so ya ke yi mata amma har yanzu ya kassa yarda da hakan , Idan har AMIR ya bude baki ya ce ya na son yarinyar nan zan fi kowa farin ciki , she is so innocent , abun da na lura da shi ta fi yar uwarta nitsuwa , za su dace sosai da juna , Sai dai kashh ya ki karbar soyayyar da ke cikin zuciyar shi " " To yanzu Ammie ya ki ke so mu yi " shiru MALIKAT INAS ta yi na dan lokaci kafin ta ce " ba abun da za mu yi , kawai za mu sakawa ikon Allah ido , Tun da har ya hada su , Haka zalika zai sa soyayyar da ke cikin zuciyar AMIR ta fito fili , na mu kawai mu taimaka musu idan za mu iya " kara fadada murmushin ta RIANNA ta yi ta na fadin " Ammie Allah ma ya ce tashi na taimake ka , dole sai mun saka Hannu cikin lamarin su " " To ya ki ke so mu yi , ni fa ban taba jin AMIR ya bude baki ya ce ga kalar matar da ya ke so bare har mu yi wani kokarin sauya ta " " no Ammie ba wani sauyawa , a hakan ma ta yi , ni dai na san AMIR ya na son mace mai kwaliya , ba ki lura da irin kallon da ya ke yi mata dazu da safe , ni dai na san ko bai fada ba , kwaliyar ta ta burge shi " yar karamar dariya MALIKAT INAS ta yi kafin ta ce " Oh dama kin san da wannan shi ya sa ki ka shirya ta tun da safe haka " " me ki ke tunani na sani mana , ai duk fadin masarautar nan babu wanda ya san AMIR sama da ni , ke dai ki sha zama kawai za ki sha kallo " RIANNA ta fada cike da kwarin guyiwa allamun ta shirya wata a kassa ita dai MALIKAT INAS ba ce komai ba kawai ta zuba wa Inaya idanu ▪AMIR bayan ya fito part din MALIKAT INAS kai tsaye part din Malik ya wuce , kafin ya shiga sai da ya cire Alkyabar shi ya mikawa Azim da ke biye da shi sannan ya shiga building din kai tsaye hawa na biyu ya nufa , nan ya tardo Malik tare da wasu manyan mutane biyu ko gaishe su bai yi ba , sallamar shi ma shi kadai ya ji abu ne kai tsaye ya nufi wata sofa ya zauna , zaman nan irin na gasaita sai da ya zauna sannan Malik ya ce mishi " AMIR , Azim bai fada maka ka same ni a fada ba " cikin ko in kula AMIR ya ce " ya fada min " " Me ya sa ba ka je ba to , saboda kai musaman na shirya zama amma ba ka zo ba " Malik ya fada ya na nuna bacin ran shi a hankali AMIR ya gyara zaman shi ya na fadin " Next time " dan murmushi Malik ya yi ya na gyada kan shi kafin ya ce " okay na san ba za ka manta da wadanan nan ba , Sarkin Dogarai Hussein Bin Hashim da kuma Sarkin Bayi Mohammed Magid " gyada kan shi a hankali AMIR ya yi kafin ya ce " Yes ban manta da su ba , ba wannan ne ba ya taba tsula min bulalar bayin shi ba " ya fada ya na nuna Sarkin bayi da ido a tare duk su ka yi dariya sannan Sarkin bayi ya ce " To ina neman Afuwar Yarima , akasi ne a ka samu a ranar " dan tabe baki AMIR ya yi ya na kauda kan shi gefe sai da su ka tsagaita dariyar su sannan Malik ya ce " Kar ka manta matsayin uncle din ka su ke " cikin nitsuwa AMIR ya katse shi da cewa " Abbi ba sai ka fada ba na sani , wannan shi ya ke auren MALIKAT MANISHA yarinyar MALIKAT HOUDA , Wannan kuma Yarinyar MALIKAT YOUSSRA " ya fada ya na nuna Sarkin bayi da ga karshe Jinjina kan shi Hussein ya yi kafin ya ce " Ashe dai ba ka manta da mu ba " " no " ya fada a takaice kafin ya mike ya nufi lift ya shiga ya nufi hawa na uku , ya na hawa ya wuce kai tsaye bedroom din shi A cen kassa kuma inda ya baro Malik , sai da su ka Kamala tatauna war su a kan matsalolin da su ka shafi masarautar sannan ko wane ya tashi ya kama aikin gaban shi ▪NESRINE bayan sun baro AMIR da Inaya kai tsaye part din MALIKAT HOUDA su ka nufa A tare duk su ka yi sallama kafin su ka karaso cikin parlourn inda MALIKAT HOUDA ke zaune saman sofa ga table a gaban ta shake da fruits a gaban ta su ka zube saman guyiwowin su sannan Diya ya ce " gaisuwa na ke ya shugaba ta " dan karamin murmushi MALIKAT HOUDA ta yi kafin ta ce musu su tashi ita ba ta son wannan gaishe gaishen na shirme yar karamar dariya Diya ya yi kafin ya ce " An gama ran ki shi dade , dama mun zo ganin mahaifiyar su ne " " ka ce yaran Amina ne , Masha Allah , sannun ku to , tashi ku je ta na cikin daki na uku " MALIKAT HOUDA ta fada ta na murmushi , matar nan ba ta da matsala sam ita kowa na ta ne dalilin da ya sa ma AMIR ya ce a kawo mama wajen ta ba musu su ka tashi su ka nufi corridor din bedrooms su ka shiga ta uku nan su ka tardo mama zaune saman gadon ta , ta kurewa waje guda ido kamar mai tunanin wani abu Nesrine na ganin ta yi gudu ta fada jikin ta na sakin kuka sai a lokacin mama ta dawo cikin hayacin ta , ta daura hannun ta guda saman bayan Nesrine ta na fadin " lafiya ki ke kuka tun da safe haka " a hankali Nesrine ta dago da ga jikin mama ta kai hannu ta fara goge hawayen ta , ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " ba komai mama kawai na yi kewar ki ne " dan karamin murmushi ita ma mama ta yi kafin ta juya ta kali Diya da Abdoul da ke tsaye bakin kofa ta ce " Abdoul , Moussa ku nan za ku tsaya " yar karamar dariya Abdoul ya yi kafin ya karaso cikin dakin ya na fadin " mama ba fa sunan shi Moussa , sunan shi Diya " " Toooo , da gaske ne malam Moussa " Mama ta fada ta na kallon Diya dan karamin murmushi ya yi kafin ya gyada mata kai allamun eh da ga haka kuma ya ce " ni zan koma , zan dawo inda na samu dama " ya na gama fadar haka ya juya zai bar dakin sai da ya fita sannan mama ta kali Nesrine murya kassa kassa ta ce " ba za ki tashi ki raka shi ba " turo dan bakin nan nata ta yi ta na shirin magana mama ta riga ta cewa " idan ba ki tashi ba sai na sabba miki " ai ko ta na jin hakan ta yi sauri ta tashi ta bi bayan Diya ta ko yi sa'a bai gama fita corridor din ba sai ta yi mishi gyaran murya sama sama cak ya tsaya ya juyo a hankali , ya na ganin ita ce ya saki wani cool murmushi ya ce mata " lafiya ? ki na bukatar wani abu ne " A hankali ta girgiza mishi kai kafin ta fara takowa gare shi a hankali ta tsaya gaban shi ta dan sunkuyar da kai ita ta ma rasa abun da za ta ce mishi dan karamin murmushi ya saki kafin ya kai hannu saman habar ta ya dago kan ta , ba shiri ya kai dan bakin shi saitin kumatun ta ya yi mata kiss sannan ya ce " ni ma zan yi kewar amma ba zan jima ba " ya na gama fadar haka ya janye hannun shi ya juya ya ci gaba da tafiyar shi ita dai malama Nesrine ta yi sumar tsaye abun da ta zo fada daban abun da ya gane daban , a hankali ta dago hannu ta daura saman kumatun ta ba ta san lokacin da wani cool murmushi ya subce mata ba , da sauri ta kai hannayan ta biyu ta boye fuskar ta ta na ci gaba da murmushin ta wai ita ta ji kunya ( da ga baya kenan 🤣🤣🤣🤣 ) sai da ta gama tsayuwar ta sannan ta juya ta koma dakin mama ta na shiga ta Haye saman gadon baki daya ta konta ta tada kai da cinyar mama dan karamin murmushi mama ta yi kafin ta daura hannun ta saman kan Nesrine ta ce " ina ku ka baro min auta " murmushi mai dan sauti Abdoul ya yi kafin ya ce " su na tare ita da Zayd " " ina son Ganin su don Allah " mama ta fada ta na marairaice fuska yar dariya Abdoul ya yi kafin ya ce " mama ni dai yanzu tsakani na da Zayd sai dai gaisuwa , wlh ba zan iya tafiya ba na ce ki na neman sa , karfi na bai kai cen ba , ita dai Auta ba matsala Nesrine sai ta kirawo miki ita " " To abun har ya kai haka yaushe ka fara jin tsoron Zayd " mama ta fada cikin zolaya [16/09 à 09:57] M.N.M: ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】 ____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________ {PAGE _______8❤🔥} ta na gama fadar haka ta bace bat a wajen ( bari dai mu bi ta mu ji ina ta tafi 🤔🤔 ) sai ga ta nan tsaye ta bayan masarautar wajen da ko guards babu a wajen ita kadai tsaye kasan wata katuwar bishiya ta na tsaye a haka wani mutun ya fito zaune a kassan bishiyar , Ya na sanye da wadanan kayan na shi bakake , kamar dai kullum fuskar shi a rufe ta ke , da rawanin nan baki , idanun shi kadai a ke iya gani a hankali ya bude baki ya ce " lafiya ki ka kirawo ni " cike da bacin rai Rouksar ta ce mishi " Damba , akwai matsala fa , yarima ya na tare da wata shegiyar yarinya da ta lake mishi , shi kuma ba ya ce mata komai " cikin ko in kula Damba ya ce mata " sai me , kema ba mace ba ce ki jawo hankalin shi mana , kar ki sake kira na da wannan shirmen , ba da zama ki ka shigo masarautar nan ba , mulkin saudiya za ki amso mana dan haka ki tashi ki yi aikin da ya kawo ki , ko kuma " ya na gama fadar hakan ya ga wani dankareren maciji ya nufo shi ya na neman ya sare shi cikin zafin nama ya damko kan macijin nan ya na kallon Rouksar ya ce mata " ke Medusa , ki kula da abubuwan wasan ki " ya na gama fadar haka ya tila mata macijin a fuska da ga nan ya bace a wajen ya bar nan tsaye kamar da wassa macijin nan ya koma cikin gashin ya bace bat cikin jelar , nan take ita ma ta bace , sai ga ta dawo cikin toilet kofar ta nufa ta bude ta ta fito , kai tsaye bedroom din ta fito ta dawo cikin parlourn inda ta bar tesnim ko motsi ba ta yi ba , ko sannu ba ta ce mata ba ta nufi wajen da ta taso ta koma ta zauna ta dauki wayar ta * AMIR zaune su ke cikin dining room din part din Malik , kamar dai kullum abincin dare a tare su ke cin shi tsawan shekaru yanzu rabon su da su yi diner tare da Amir , musaman Malik ya ba da umarni a shirya duk wani abinci da Amir ke so , Table din a shake ta ke kamar unguwa guda za ta ci abincin , amma su shidda ne kadai wannan uban duniyar abincin su su ke ci cikin konciyar hankali babu wanda ya ce ko ufan su na a haka Malik ya katse shirun su da cewa " Ina son ku ba ni hankalin ki duka , zan so na yi muku wata magana " a tare Malikat Inas da Malikat Al'umu su ka hada baki wajen cewa " Wace magana ce wannan kuma ? " dan jinkirtawa Malik ya yi kafin ya ce " Daya da ga cikin yaran da Amir ya dawo da su Matar shi , tsawan shekara biyu yanzu da yin auren su , ba na son jin korafin kowa a nan , Malikat Inas MALIKAT AL'UMU ku na ba wa hakin kulla da ita , ina son ku koya mata duk wani abun da ya dace , bayan dawowar mu da ga Makka za ta dawo dakin mijin ta " baki sake Tesnim da MALIKAT AL'UMU ke kallon Amir su na zaro idanu RIANNA da MALIKAT INAS ko sai murmushi su ke yi dama sun san da maganar auren sarai ya lura da su amma bai ce musu ko ufan ba , Ya ci gaba da cin abincin shi su na a haka su ka jiyo Muryar Malik ya na kiran Azim da sauri Azim ya karaso wajen Malik ya Zube saman guyiwowin shi cike da girmamawa ya shiga gaishe su baki daya daga mishi hannu Malik ya yi allamun ya yi shiru sannan ya ce " je ka kira min yarinyar da ke part din MALIKAT INAS , karamar " ya na gama fadar haka Azim ya mike da gudu ya fice parlourn ya bar building din baki daya ya nufi part din Malikat INAS ya na barin wajen Malik ya kali Amir ya ce " Nawfel ? " slowly Amir ya dago kai ya kali Malik ba tare da ya ce komai ba cike da zolaya Malik ya ce " Ba ka da abokin da zai raka ka dakin amaryar ka , ko na kai ka da kai na " shiru Amir ya yi bai ce komai ba , a hankali ya tashi da ga saman kujerar shi ya juya da sauri RIANNA ta ce " Akhie , wassa fa Abbi ke yi maka " ko juyowa bai yi ba ya ci gaba da takawar shi ya koma parlourn ya zauna saman doguwar sofa ya fido wayar shi da ga cikin aljihun shi ya fara latsawa yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya ce " na ga allamun ke za ki raka shi dakin Amaryar shi ! " RIANNA na shirin magana TESNIM ta riga ta cewa " a'a Abbi , ni da ita za mu tafi " ta kai karshen ta na kashewa Rianna ido guda a tare su ka yi yar karamar dariya duk abun da su ke yi Amir ya na jin su amma bai tanka musu ba su na a haka Azim ya shigo parlourn ya na sallama Inaya na biye da bayan shi a tare su ka karaso cikin parlourn ta na ganin Amir ta saki wani kyawatencen murmushi da gudu ta nufe shi ta rungume shi ta na fadin " yaya Zayd tun dazu ina ta jiran ka amma ba ka zo ba " ajiye wayar shi gefe ya yi a hankali ya sa hannayan shi biyu ya dago ta da ga jikin shi ya ce mata " ba ki ga mutanan da ke wajen ba " slowly ta juyo da kan ta , ta kali saitin da su Malik ke zaune , sun ko tsare su da idanu babu ko kiftawa dum Inaya ta ji zuciyar ta buga da sauri ta boye fuskar ta a bayan Amir " tashi ki je Abbi na son magana da ke " ya fada mata cen kassan makoshi a hankali ta girgiza mishi kai ba tare da ta ce komai ba allamun ba za ta je ba " please tashi ki je , ba abun da zai miki " a hankali ta fido kan ta da ga bayan Amir , ta mike a hankali ta nufi su Malik zuciyar ta na duka uku uku ji ta ke yi kamar ta yi kuka , ko ta juya da gudu ta bar wajen amma ba hali a haka ta karaso gaban Malik ta sunkuyar da kai Muryar ta har kerma ta ke yi ta ce " Bar.....barka da da da....re " Malik na shirin magana Tesnim ta ce " Akhie wannan ita ce matar ta ka " ta kai karshen ta na yi ma Inaya wani kallon wulakanci Da sauri Malik ya taka mata burki ya na cewa " ke Tesnim ki shiga tayi'tayin ki , wannan matar Yayan ki ce " cikin nitsuwa MALIKAT AL'UMU ta katse shi da cewa " ran ka shi dade , na ga wannan ai ko TESNIM ta girme ta , ta ya za ta zama matar Amir din Saudiya guda " " Nawfel Hicham Bin Jaabar , ka dauke ta a matsayin matar ka , ko kuwa " Malik ya fada cike da Izza , da Allamun yanzu da Al-MALIK HICHAM BIN JAABAR su ke tare ba mahaifin su ba yanayin da ya yi maganar ya sa su duk shan ruwan jikin su , su ka sunkuyar da kai Shiru Amir ya yi bai ce komai ya na kallon kassa ya na a haka ya sake jiyo Muryar Malik ya na fadin " Nawfel da kai na ke magana " slowly ya bude baki shi ya ce " eh " a takaice wani kyawatencen murmushi ne MALIKAT INAS da RIANNA su ka saki a tare sun samu abun da su ke so Malik kuwa juyo wa ya yi ya kali MALIKAT AL'UMU ya ce " Kin karbe ta a matsayin Sirikar ki ? " dan karamin murmushi MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta ce " Tun da Amir ya yarda , ni ma ban da ja a kai , na karbe ta " a hankali Amir ya Lumshe idanun shi ya na sauke ajiyar zuciya , shi dama har ga Allah ya na tsoron su ce ba za su karbe ta a matsayin matar shi ba amma tun da sun karbe ta komai ya yi mishi sauki haka zalika Malik sai da ya yi wa Allah godiya cikin zuciyar shi a hankali ya mika wa Inaya hannu ba musu ta karaso a hankali ta daura hannun ta saman na shi , hannun ta har kerma ya ke yi dan karamin murmushi Malik ya yi kafin janyo mata chair din da Amir ya tashi ya ce ta zauna ba musu ta zauna ta na sunkuyar da kai ta na zama Malik ya ce " Ba zan yarda wani ya yi mata ko da kallon da bai dace ba , kin ji dai na fada miki Tesnim " ya kai karshen ya na tsuke fuska dan ya san Halin Tesnim , ba ta da mutunci ko kadan bare in ta girmi mutum yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " Abbi ni na ma isa , ai tsakanin mu gaisuwa ce kawai " a hankali Malik ya gyada kan shi kafin ya kali Inaya da ta sunkuyar da kai ya ce " dago kan ki yarinya " shiru Inaya ta yi ko motsi ba ta yi ba da sauri RIANNA ta ce ma Malik " Abbi ba ta jin larabci , sai kun yi da Turanci " gyada mata kai Malik ya yi kafin ya yi mata magana da turanci ya ce " dago kan ki , nan duk sirikan ki ne , kar ki ji tsoro kin ji " a hankali Inaya ta gyada mishi kai kafin ta dago ta na bin su da kallo daya bayan daya sannan ta saki wani cool murmushi ta meda kan ta ta sunkuyar " in sha Allah bayan dawowar mu , da ga Makka za a gabatar da ita a matsayin matar Amir , yanzu ina son ku koya mata duk wani abun da ya shafi Daular Saudiya " Malik ya fada a tare duk su ka hada baki su na cewa " an gama ran ka shi dade " Inaya kuma a hankali ta dago kai ta kali Malik ta ce " Uncle , zan iya komawa , barci na ke ji " ta kai karshen ta na marairaice fuska dan karamin murmushi Malik ya yi kafin ya gyada mata kai sannan ya kali Amir cikin harshen larabci ya ce mishi " Nawfel , tashi ka meda ta part din MALIKAT INAS " a dubu dari Amir ya dago kan shi ya kali Malik ya na zaro idanu da sauri Malik ya daga mishi hannu ya na fadin " idan ba za ka tashi ba , ni na tashi da kai na " dan karamin tsaki Amir ya yi ya na kauda kan shi gefe sannan ya tashi ya nufi hanyar fita wajen yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya kali Inaya ya ce " za ki iya tafiyar ki " dan karamin murmushi Inaya ta yi kafin ta mike da ga saman Chair din ta nufi hanyar fita wajen ta bi bayan Amir a tare shi da ita su ka baro Building din , ta na tafe ta na hamma allamun ta na jin barcin sosai duk abun da ta ke ya na lure da ita amma ya kyale ta a haka har su ka karaso cikin part din MALIKAT INAS su na shigowa parlour su ka tardo Diya tare da Nesrine su na zaune a kassa su na hirar su gwanin burgewa Amir ya ganin shi ya kara tsuke fuska , bai ce mishi komai ba su ka nufi corridor har sai da ya raka ta cikin bedroom din ta Diya na ganin shi amma bai ce mishi komai ba har sai da su ka shiga corridor sannan ya yi wata yar karamar dariya Amir kuma su na shiga cikin bedroom din ta ya ce mata " sai dai safe " ya kai karshen ya na juyawa bai yi taku daya ba ya jiyo Muryar ta ta na cewa " yaya Zayd ba za ka zauna ba " slowly ya juyo ya kale ta ya ce " me za ki ba ni in na zauna ? " da sauri ta kai hannu ta bude box din bedside drawer ta fido sweet biyu ta nuna mishi ta na murmushi a hankali ya girgiza mata kai ya ce " ba na shan sweet " turo dan bakin nan nata ta yi cike da shagwaba ta ce " Don Allah kar ka tafi yaya Zayd " ta kai karshen kamar za ta yi kuka , har sai da idanun ta su ka ciko da ruwa cikin konciyar hankali ya tako ya karaso bakin gadon ya zauna ba dan ya so ba , ba zai so ya ga kukan ta ne cikin wannan daren , ya san ba zai samu nitsuwar yin barci ba in har ta yi mishi kuka ta na ganin ya zauna ta yi sauri ita ma ta Haye bed din duka , ta zauna a tsakiya ta yi zaman cin turo ta na murmushi ta ce " yaya Zayd na gwada maka wani abu " a hankali ya gyada mata kai allamun eh da sauri ta daga pillow din gadon ta dauko wata tsadadiyar phone kirar Iphone 14 pro max , mai launin Gold sabuwa fil har wani kyali ta ke yi dan zaro idanu ya yi ya kai hannu ya karbi wayar ya na fadin " wa ya ba ki wannan ? " " Aunty RIANNA ce ta saya mana ni da Nesi " a hankali ya gyada kan shi ya na kunna wayar , nan ya ga akwai card Sim a ciki contact ya shiga ya ga babu number ko guda a ciki bai tsaya wani tunanin ba , ya saka number din shi ya yi saving din ta ( ni dai ba zan fada muku sunan da ya saka ba gaskia 🤭🤭🤭 ) bayan ya yi Saving ya danna wa kan shi kira nan take wayar shi da ke cikin aljihun shi ta fara ringing , hannu ya kai ya fido wayar sannan ya kashe kiran ya mika mata wayar ta , Sannan ya shiga latsa ta shi ya ce mata " Idan na tafi zan dinga kiran ki ga number ta na saka miki , ko ki na bukatar wani abu sai ki kire ni " " shikenan yaya Zayd " ta fada ta na ajiye wayar saman bedside drawer meda wayar shi shi ma ya yi cikin Aljihu kafin ya ce " ki dai na kira na da yaya Zayd ba shi ne ba sunana " a hankali ta matso kusa da shi ta ce " to minene Sunan ka " " Nawfel " ya fada mata a takaice " Zayd ba sunan ka ba ne , kuma ai na ji yaya Moussa ya na kiran ka da Amir " " Zayd sunan kaka na ne , Shi ya sa Diya ba ya iya kira na da sunnan sai dai ya ce Amir " ya na gama rufe bakin shi ya ji ta zagayo da hannayan ta ta baya ta rungume shi , ta kontar da kan ta saman bayan shi ta na fadin " ni dai da yaya Zayd zan ci gaba da kiran ka , ni da wannan sunnan na san ka , kuma , shi zan rike " hmm ita ba ta san Amir ya riga da ya bar duniyar mutane ya na jin ta zagayo da hannayan ta ya dauke kamar wutar nepa cen cikin zuciyar shi ya ce " yarinyar nan ta na shirin kashe ni wlh " [16/09 à 09:57] M.N.M: ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………………… 2 ❤ 👑✌】 ____________________🕊🌹🕊🌹🕊🌹🕊🌹🕊🌹🕊🌹🕊🌹🕊🌹___________________ {PAGE _______7 ❤🔥} yar karamar dariya Abdoul ya yi kafin ya ce " mama ni fa ba tsoron shi na ke ba , kawai dai yanzu ya fi karfin na je a na kiran shi , sai dai shi ya kira mu " shiru mama ta yi ba ta ce komai ba ta na ci gaba da shafa kan Nesrine da barci ya dauke ▪AFTER SOME HOURS ▪AMIR zaune su ke shi da Malik a cikin parlourn su da ke hawa na uku su na zaune bakin Glass su na kallon Masarautar su na a haka kawai su ka ga Inaya ta fito da ga part din MALIKAT INAS , ta na sanye da wata gown fara kal mai mugun kyau ba ta daura Alkyaba ba , ta saki wannan lalawsan gashin kan ta ya zubo mata har tsakar baya ta na tafiyar ta cikin konciyar hankali tun da ta fito AMIR ya tsare ta da wadanan hazel eyes din na shi har maganar da Malik ke yi mishi komai bai ji ba a hankali Malik ya juya kan shi ya kali saitin da AMIR ke kallo nan ya ga Inaya ta na tafiyar ta a hankali cikin masarautar gwanin burgewa dan karamin murmushi Malik ya saki kafin ya kai hannun saitin fuskar AMIR ya kyasta mishi yatsun a hankali AMIR ya lumshe idanun shi kafin ya bude su ya juya ya kali Malik ya na daga mishi gera guda allamun minene " me ka ke kallo ne haka tun dazu na ke yi maka magana amma hankalin ka ba ya tare da ni " juya kan shi AMIR ya yi ya na fadin " nothing " a takaice " shikenan fada min me ke tsakanin ka da yarinyar cen da ka tsare da ido " Malik ya fada ya na daga mishi gera kamar ya na kallon shi dan jinkirtawa AMIR ya yi kafin ya bude bakin shi murya kassa kassa ya ce " She is my wife , your daughter-in-low , ko ka na da ja ? " a dubu dari Malik ya mike tsaye ya na fadin " what , Matar ka fa ka ce min AMIR , yaushe hakan ta faru " ba tare da ya juyo ya kale shi ba ya ce " two years , Tsawan shekara biyu yanzu da yin auren " wani kyawatencen murmushi ne Malik ya saki ya na komawa ya zauna saman chair din shi ya ce " ba banza ka ki dawowa , ashe yarinyar mutane ka samu " shi dai AMIR shiru ya yi bai ce mishi komai ba ya ci gaba da kallon Inaya " Bayan dawowar mu da ga Makka za ta dawo part din ka da zama " Malik ya fada ya na kallon AMIR a hankali AMIR ya juyo ya kali Malik ya ce " Makka kuma ? " " eh , ko ka manta tafiyar da mu ke yi duk watan azumi ? " dan lumshe idanun shi AMIR ya yi shi ya ma manta da wannan tafiyar da su ke yi shi da Malik , shi gaskia ba ya jin zai iya yin tafiyar nan ya bar Inaya a cikin masarautar nan ita kadai a hankali AMIR ya bude idanun shi , har ya bude baki zai yi magana , ya rufe bakin shi ya tashi a hankali ya bar wajen da kallo Malik ya raka shi har sai da ya fice bai ce mishi komai ba ▪INAYA a hankali ta ke tafiyar ta cikin masarautar , ga wani kyawatencen murmushi konce saman fuskar ta , ta na tafe ta na dube duben ta , har ta karaso cikin garden ta na tsaka da tafiyar ta kawai ta ji ta buge mutun a hankali ta dago kai ta na kallon ta Rouksar ta na saki wani cool murmushi ta ce mata " Yi hakuri ban gan ki ba ne " ta kai karshen ta na shirin rabawa ta geffen Rouksar za ta wuce ba shiri ta ji an riko hannun damtsen ta cak Inaya ta tsaya ta juyo ta na kallon Rouksar a hankali Rouksar ta dawo Gaban Inaya ta tsaya sannan ta fara yi mata kallon wulakanci ita dai Inaya shiru ta yi ba ta ce komai ba sai da ta gama kallon na ta sannan Rouksar ta ce mata " kar na sake ganin kusan AMIR " cikin rudu Inaya ta ce mata " wanene AMIR kuma ? " wata yar karamar dariya Rouksar irin ta rainin hankali kafin ta ce ma Inaya " kin ma raina min hankali yarinyar nan , ki na nufin ba ki san wanene AMIR ba " a hankali Inaya ta girgiza mata kai allamun a'a " shikenan tun da ba ki san shi ba , amma zan fada miki wani abu , kar ki kuskura ki ce za ki shiga gona ta , Idan kuma ki ka shiga , za ki iya rasa rayuwar ki , idan kunne ya ji , jiki ya tsira " ita dai Inaya da ido kawai ta ke bin dan ba ta ma san maganar me ta ke yi ba Rouksar kuma ta na gama fadar haka ta raba ta geffen ta ta wuce har ta yi taku biyu ta tsaya cak , a hankali ta juya ta ga ita ma Inaya har ta juya wani murmushin mugunta ta saki kafin ta juya ta kai hannu ta tura Inaya ta fadi kassa wata yar karamar kara Inaya ta saki ta na dago kai ta kali Rouksar nuna ta da dan yatsa Rouksar ta yi ta na fadin " wannan kadan ma ki ka gani duk ranar da na sake ganin ki tare da shi sai na yi miki abun da ya fi haka " ta na gama fadar haka ta juya ta ci gaba da tafiyar ta da kallo Inaya ta rakata har sai da ta bar wajen sannan ta murguna mata baki ta na yi mata gwalo kamar kamar yarinya sannan ta fara kokarin mike wa tsaye , sai dai wajen tashi ta taka gown din ta , nan take ta yage har zuwa saman cinyar ta nan take idanun ta su ka kawo ruwa , ta kai hannu ta matse tsagar kamar ta yi kuka ta ce " Allah ya isa , muguwa kawai " kamar da ga sama ta jiyo Muryar AMIR da ga bayan ta ya na fadin " ke da wa kuma ? " a razane ta juyo ta na kallon shi idanun ta cike da ruwa da gudu ta fada jikin shi ta rungume shi ta na sakin kuka ta ce " yaya Zayd ba wacen yarinyar ba ce , ban yi mata komai ba ta tura ni na fadi yanzu ga shi riga ta ta cire " a hankali ya kai hannu ya dago ta da ga jikin shi ya na fadin " shikenan mu je ki sauya rigar " rage sautin kukan ta ta yi ta na fadin " yaya Zayd ta fa yage sosai , ba zan iya tafiya a haka , kuma ka na gani b...... " ba ta karasa maganar ta ba ta ji ya sa hannayan shi biyu ya dauke ta cak kamar baby , ba tare da ya ce mata komai ba ya nufi part din MALIKAT INAS shiru ta yi ta na kallon Face din shi , yadda ya sauya mata lokaci guda kamar ba shi ne yaya Zayd din ta ba duk in da ya wuce sai guard sun sara mishi , in kuma dogarai ne sai sun runsuna sun sunkuyar da kai su na bin shi da kallo ta wutsiyar ido Amir kuwa ko a jikin shi ya na dauke da babyn shi a haka har su ka iso part din MALIKAT INAS babu ko sallama ya shigo parlourn MALIKAT INAS , su na zaune ita da RIANNA su na ganin shi dauke da Inaya su ka saki wani kyawatencen murmushi a tare , su ka raka shi da ido babu wanda ta ce mishi ufan har ya shige corridor ya na shiga corridor murya kassa kassa ya ce ma Inaya " where is your bedroom ? " da yatsa ta nuna mishi bedroom din da su ke ciki ita da Nesrine bedroom din ya nufa ya sa kafa ya tura ta sannan ya shiga bakin gadon ya karaso sannan ya sauke ta saman kafafun ta ya na fadin " Shikenan yanzu tafi ki sauya kayan a karamin murmushi ta yi ta na gyada mishi kai kafin ta juya ta fara takawa duk taku daya in ta yi sai wadanan santala santalan cinyoyin na ta sun fito da sauri AMIR ya kauda kan shi dan fa ya ga abun 🤣 har ta kai bakin kofar Dressing room ta jiyo Muryar shi ya na fadin " tsaya " cak ta tsaya da tafiyar ta ta juyo ta kale shi ta ce " lafiya yaya Zayd " girgiza mata kai ya yi allamun ba komai kafin ya ce mata ta dawo ba musu ta dawo gaban shi ta tsaya ta na murmushi shiru ya yi bai ce mata komai ba ya zuba mata wadanan idanun na shi sai da ya dan dauki lokaci a haka kafin ya daga kafa a hankali ya juya ya nufi kofar dakin a tunanin ta fita zai yi , kawai sai ganin ta yi ya meda kofar ya rufe , sannan ya juyo ya karaso bakin gadon ya zauna ita dai Inaya da ido kawai ta ke bin shi , ta na murmushi , ba ta san abun da ya ke shirin aikatawa ba a hankali ya mika mata hannun shi ya na kallon cikin idanun ta ba musu ta daura hannun ta saman na shi ta na ci gaba da murmushin ta kafin ta tako ta tsaya dab gaban shi a hankali ya janyo ta ya zaunar da ita saman cinyar shi murya kassa kassa ya ce mata " Saura kwana nawa a fara azumi " a hankali ta daga kan ta sama , ta hura kumatun ta na a haka kawai sai ji ta yi ya daura mata yatsar shi saman kumatun ta ya dan danna ba ta san lokacin da wata yar karamar dariya ta kubce mata ba " tambayar ki na yi ban ce ki hura min kumatu ba " ya fada mata ya janye hannun shi " Yo ai yaya Zayd tunani na ke yi " ta fada cikin shagwaba " shikenan kin samo ? " " eh saura sati guda ina ji " gyada mata kai ya yi a hankali , ya kai hannun shi ya riko nata ya ce " yeah , saura sati guda , ni da Malik za mu yi tafiya zuwa Makka , a cen mu ke yin azumi ko wace shekara " da sauri ta katse shi da cewa " Yaya Zayd yanzu tafiya za ka yi ka bar ni ? " ta fada idanun ta su na kawo ruwa nan take ta fara ruwan hawaye A hankali ya kai hannu ya kontar da kan ta saman shoulder din shi cikin sigar rarrashi ya ce mata " don't worry , bayan watan azumi zan dawo kuma ba yanzu ba zan tafi ki kontar da hankalin ki " zagayo da hannayan ta ta yi a wuyan shi ta na sakin dan karamin kuka a hankali ya lumshe idanun shi ya na jin zuciyar shi ba dadi har ga Allah ba ya son jin kukan ta ga shi ba wani rarrashi ya iya ba bare ya ce ya rarrashe ta , haka kawai ya tsaya ya yi shiru ya na sauraron yadda ta ke kukan ta kassa kassa slowly ya sauko da hannun shi da ga saman kan ta bai sauke shi ko ina ba sai saman cinyar ta , dama tun zaman da ta yi ta fito Wani irin shock ne ya ji lokacin da hannun shi ya sauka saman fatar jikin ta , luwai luwai da ita ga taushi kamar ta baby , nan take ya ji wani zir tun da ga tafin kafar shi har tsakiyar kan shi , duk wata siga ta jikin shi sai da ta mike , duk wasu kofofin feelings din shi sai da su ka bude lokaci guda a hankali ya fara shafa cinyar ta ido a lumshe , ya kontar da kan shi saman shoulder din ta ya na a haka kawai ya ji ta sauke wata nanauyar ajiyar zuciya har sai da ya ware idanun shi ba shiri ya na bude idanun shi ya ji fara yo kassa da hannun ta guda ta daura shi saman kirjin shi a hankali ya bude baki ya ce mata " me ki ke so na sayo miki idan na je " murya cen kassan makoshi ta ce mishi " duk abun da ya burge ka ina so " " shikenan yanzu tashi ki je ki sauya rigar ki " ya fada ya na dago kan shi da ga saman shoulder din ta a hankali ita ma ta dago ta kale shi sai da gaban ta ya fadi lokacin da ta ga yadda idanun shi su ka koma jazir " yaya Zayd me ya samu idanun ka , su ka yi ja haka ? " ta fada ta na daura hannu ta saman kumatun shi dan lumshe idanun shi ya yi kafin ya sake bude su a hankali saman ta , murya cen kassan makoshi ya ce mata " Ba komai tashi ki tafi " dan karamin murmushi ta yi kafin ta janye hannun ta , ta tashi da ga saman cinyar shi ta nufi dressing room , har za ta shiga ta juya ta nufi toilet ta shiga ta rufe kofar da kallo ya rakata har sai da ta rufe kofar toilet din sannan ya tashi a hankali ya nufi kofar fita dakin ya ficewar shi ya na fitowa parlourn ya nufi kofar fita part din har ya kai bakin kofa ya jiyo Muryar MALIKAT INAS ta na fadin " AMIR me ya same ka ? ka sauya lokaci guda " ba tare da ya juyo ba ya ce mata ba komai , da ga haka ya daga kafa ya fice part din da kallo ta raka shi har sai da ya fice sannan ta saki wani cool murmushi * ROUKSAR zaune su ke ita da Tesnim cikin parlourn part din MALIKAT AL'UMU , ga uban Fruits a gaban su , ko wace na rike da wayar ta sai faman chating su ke yi sun dan jima a haka kafin Rouksar ta ajiye wayar ta ta kali Tesnim ta ce " Amira , wai wacece yarinyar nan da na ga ta konta a jikin Amir , kuma bai ce mata komai ba " ba tare da ta ajiye wayar ta ba tesnim ta ce mata " Ni ma dai ban san ta ba , amma tare da Amir ta ke , a wajen su ya zauna tsawon shekarun nan , shi ya sa ki ka ta na lake mishi , really she is so cute , she looks so innocent " dan tabe baki Rouksar ta yi kafin ta ce " Kamar ya , yanzu haka za ki sa mata ido ta na lakewa Amir , ki taka mata burki mana .... " cikin nitsuwa Tesnim ta katse ta da cewa " Why zan yi haka ? Tun da Amir ba shi da matsala da hakan , ba na da hakin shiga lamarin shi , na san ba karamin aikin shi ba ne yanzu da na fada mata wani abu ya yi min mugun fada " ta na kai karshen maganar ta , ta saki wata yar karamar dariya " Tesnim , kin fin kowa sanin wanene Amir , Ba girman shi ba ne a ce wannan yar karamar yarinyar ta makale mishi , he is the successor of MALIK HICHAM BIN JAABAR shugaban kassar Saudiya baki Daya " ajiye wayar ta Tesnim ta yi , ta dan matso da face din ta ta ce ma Rouksar " kin ga ko , ga kofa cen bude , ban tare ki ba , tashi ki je ki fada mishi hakan , amma kin ga ni , wlh ko kashe ni a ke yi ba zan taba shiga abun da ya shafi Amir " ta na gama fadar haka ta dauki wayar ta ci gaba da aikin ta na chat wani mugun kallo Rouksar ta wurga ma Tesnim , maganar ta ta yi matukar kuna mata rai a hankali Rouksar ta mike ta na fadin " zan je toilet ina zuwa " da to kawai Tesnim ta amsa mata ba tare da ta dago kai ba sai da Rouksar ta harare ta sama da kassa kafin ta daga kafa ta nufi corridor din bedrooms , ta nufi bedroom ta farko , ta shiga ta meda kofar , sannan ta nufi toilet ta shiga ta meda kofar ta sa key ta na shiga ta saki wata yar karamar kara ta na fadin " sai na yi maganin ki yar rainin hankali " ta na gama fadar haka ta bace bat a wajen babu ita babu mai kama da ita 😨😨😨 KU TSAYA NA KORA RUWA ABUN YA FARA FIN KARFI NA [16/09 à 18:17] M.N.M: ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】 ____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________ PAGE 9 ❤🔥 da sauri ya sa Hannayan shi ya janye na ta , ya tashi da sauri ya fice dakin a rude ta ke kiran sunan shi , amma ina ko sauraron ta ba ya yi , ya fice dakin da sauri ya fito corridor din ya shigo parlour har Diya ya yi tafiyar shi , MALIKAT INAS da RIANNA sun dawo su na nan zaune parlourn tare da Nesrine su na ganin yadda ya fito corridor din ya na saurin nan su ka san ba lafiya ba ko ta kan su bai bi ba ya sa kafa ya fice parlourn ya fita part din baki daya ya na fita MALIKAT INAS ta kali RIANNA ta ce mata " Tashi ki dubo kar a je Zuciya ta debe shi , ya buge ta bai sani ba " da sauri RIANNA ta tashi ta nufi corridor ta shiga bedroom din Inaya babu ko sallama ta na shiga ta ga Inaya konce saman gadon ta , ta na latsa wayar ta ga sweet a bakin ta cike da rudu RIANNA ta ce mata " Inaya , lafiya na ga Amir ya fita da sauri haka ba dai wani abu ki ka yi mishi ba " a hankali Inaya ta girgiza mata kai ta na fadin " Aunty RIANNA ni ma ban sani ba , kawai na ga ya tashi ya fice " " shikenan zan tambaye shi " RIANNA ta fada ta na shirin juyawa da sauri Inaya ta ce mata " Aunty " cak ta tsaya ta juyo ta na tambayar ta minene girgiza mata kai Inaya ta yi kafin ta mike zaune , ta shiga cikin contact , ta nuna wa RIANNA screen din ta na fadin " Aunty mi haka ta ke nufi , ni ban gane larabci sosai " a hankali RIANNA ta kai hannu ta karbi wayar nan take ta saki wani kyawatencen murmushi ta na kallon sunnan da a ka yi register din number Amir dan ta gane numbar shi ce " Inaya wa ya saka miki numbar Amir ? " RIANNA ta fada ta na mika wa Inaya wayar ta hannu Inaya ta kai ta karba ta na fadin " yaya Zayd ya Saka min ita " " shi kuma ya saka sunnan ? " gyada mata kai Inaya ta yi kafin ta ce " eh shi ya sa na ce ki fada min me hakan ke nufi , ni ban gane abun da ya saka ba " girgiza mata kai RIANNA ta yi ta na fadin " yi hakuri ni ma ban sani ba , amma ki bari shi da ya saka , ya fada miki da kan shi " da to kawai Inaya ta amsa mata kafin ta koma ta konta ta ci gaba da game din ta a hankali RIANNA ta juya ta fice dakin ta na murmushi cikin zuciyar ta ta na fadin " Gaskia Amir ka cika dan rainin hankali " ta kai karshen dai'dai ta shigo cikin parlour MALIKAT INAS na ganin murmushin da ke saman face din RIANNA ta san ba banza ba , amma sai ta shanye dan ba ta son ta shigo cikin harkar yaran nan ▪AMIR ya na baro part din MALIKAT INAS bai tsaya ko ina ba sai building din su ya na shigowa parlourn su na uku ya tardo Malik zaune da wasu mutanan guda hudu , babu ko sallama ya shigo wajen ya nufi corridor da sauri Malik ya ce " Amir dawo ina son magana da kai " cak ya tsaya da tafiyar shi , har ya kai bakin corridor din , sannan ya juyo a hankali ya karaso cikin parlourn ya nufi sofa one seater ya zauna ya na kallon Malik ya na zama Malik ya mika mishi wasu takardun da ke gaban shi saman table da sauri Azim ya taso ya karaso wajen ya karbi takardun ya nufi Amir ya mika mishi cikin girmamawa a hankali Amir ya kai hannu ya karba ya na fadin " na minene wannan ? " kallon mutanan Hudu Malik ya yi ya ce " Wadanan dai ka san su ba sai na fada maka ba " ya fada ya na nuna Sarkin bayi , da Sarkin dogarai sannan ya nuna wanda ke kusan sarkin Bayi ya ce " wannan kuma shi ne Miram bin Salman , mai kula da Bankin Daular " sannan ya nuna na karshen ya ce " wannan kuma ,General Abdallah Mohamed , Shugaban masu tsaro , General of Army kuma , duk su na cikin mutanan Fadar Malik , kamar ko wace shekara kafin a fara azumi a na fitar da Ten Milliard , da ga Bankin Daular , dan a rabawa Al'uma , to wadanan Takardun ne ! ka san ban da gobe za mu tafi makkah , shi ya sa su ka zo dan mu tatauna a kai , zan so na ji ra'ayin ka yadda za a raba kudin " shiru Amir ya yi ya na kallon takardun ya na karantawa sai da ya karanta takardun tsab sannan ya ajiye takardun a kassa sannan ya jingina bayan shi a jikin sofar ya kali Malik ya ce " wa ke kula da raba kudin kowace shekara ? " " Sarkin bayi " Malik ya fada a takaice a hankali AMIR ya juyo ya kali Sarkin bayi ba tare da ya ce komai ba sai da ya dauki wajen good five minutes ya na kallon sarkin bayi babu ko kiftawa kafin ya ce " a ba wa MALIKAT INAS kudin wannan shekarar " " what ? " Sarkin bayi da Miram su ka fada a tare sannan Sarkin bayi ya ɗaura da cewa " tare da dukkan girmamawa Amir , Kowace shekara mu mu ke kula da wannan ta ya za a tashi rana guda a bawa wani , wanin ma....... " cikin nitsuwa Amir ya katse ta hanyar daga mishi hannu sannan ya kali Malik ya ce " ra'ayi na ka ce na fada kuma shi zan fada , ina son a duba cikin prisoner Din masarautar nan , wanda ya kusa kai karshen zaman shi , ko da ya haura wata biyar a sake shi , su koma gida jen su , zancen kudi kuma na san dalilin da ya sa na ce a bawa MALIKAT INAS , ita za ta fi sannin yadda za a yi da kudin , na san kowace shekara , da ga bayi sai dogaran masarautar nan ke samun kudin , shi ya sa na ce A kai wa MALIKAT INAS , ba ku sani ba amma yawwan cin mata sun fi wasu kaifin tunani da sanin abun da ya dace , Idan shawara ta ba ta yi muku ba , ku yi yadda ku ke so " ya na gama fadar haka ya tashi ya nufi corridor ya shige bedroom din shi ya na barin wajen Mohammed ya kali Malik ya ce " Ran ka shi dade ni dai ban yarda da wannan shawarar ba " ya na gama rufe baki Miram ya ɗaura da cewa " haka ne ya shugaba na , kowa ce shekara mu ka ke bawa ragamar kula da raba kudin nan ta ya rana guda a ce an sauya , kuma a ce mace za ta raba kudin " kallon Hussein Malik ya yi kafin ya ce " Hussein , General , me za ku ce a kai ? " " ran ka shi dade ina ga abun da Amir ya Fada dai'dai ne , ko wace shekara tsarin Raba kudin nan duk ɗaya , canjin da Amir ya kawo hakan ba karamin ɗaukaka shi zai yi , specially da ya ce a saki sauran prisoner , ko ba haka ba General " Hussein ya fada ya na kallon General gyada kan shi General ya yi kafin ya ce " Haka ne yadda ka fada , magana ta rage gare ka ran ka shi dade " a tare duk su ka kai kallon su kan Malik su na jiran su ji abun da zai ce dan jinkirtawa Malik ya yi kafin ya ce " a yi yadda Amir ya fada , za ku iya tafiya " cikin girmamawa su ka mike dukkan su , su na yi wa Malik sai da safe sannan su ka nufi hanyar fita building din baki daya ▪ MIRAM Tsaye ya ke shi da Mohammed a cikin garden din cike da bacin rai Miram ya ce ma Mohammed " Mohamed , yanzu ya za mu yi , Wacen sakaran Amir ya bata mana shirin mu " " Miram kontar da hankalin ka " Mohammed ya fada cikin nitsuwa " ta ya za ka ce na kontar da hankalin na , ni dama na San kallon nan da ya yi min ba na banza ba ne , mun jima mu na jiran wannan damar yanzu ya bata komai " wata shegiyar dariya Mohammed ya yi ya fara takawa ya yi gaba ya na fadin " kar ka damu , wannan ne na farko kuma na karshe , dan babu wanda zai dawo da ga Makka a cikin su , kai dai ka tsayar da maganar auren ka da RIANNA kafin Malik ya bar kassar nan " haka dai su ka ci gaba da tafiyar su su na hirar su ta makirci ▪AMIR Ya na jin su Miram sun fita , ya dawo cikin parlourn Malik ya na zaune inda ya ke ko motsi bai yi ba a hankali Amir ya karaso cikin parlourn ya nufi sofar da ya tashi ya koma ya zauna ya na fadin " Ina son mu yi wata Magana " a hankali Malik ya juyo ya kale shi ya ce " wace magana ? " " wanene ya nemi auren RIANNA lokacin da ba na nan " " Miram ne ! amma ta ce ba ta son shi , yanzu dai Akwai Sarki Abdoul Mujeeb ya nema wa yaron shi babba , Aymane auren ta , kuma mahaifiyar ku ta ce ta yarda ka san Abdoul Mujeeb yayan ta ne " cikin nitsuwa Amir ya katse shi da cewa " na san da wannan dukka , ina son na ga Yaron , MALIKAT INAS da ita RIANNA sun yarda ? " " yanzu dai ba ya cikin saudiya , ya tafi wani aiki a kassar Turkey , bayan Azumi ya dawo , RIANNA ta ce sai ta gan shi kafin ta yanke shawara , ka san yar uwar ta ka da mugun son maza ma su kyau shi ya sa ta ki yarda da Miram wai ya yi mata tsufa " ya kai karshen ya na yar karamar dariya " kennan babban yayan Diya ne ? " ya fada cikin zuciyar shi ya yi nisa cikin duniyar shi ya jiyo Muryar Malik ya na fadin " ya kamata ka je ka yi wa matar ban kwana yadda ya dace " slowly ya juyo da kan shi ya kali Malik ya daga mishi gera guda ya na fadin " What do you mean ? " yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya ce " ka na nufin ba za ka yi mata ban kwana ba , kar ka manta cikin daren gobe za mu tafi " " goben idan ta yi na yi mata " ya kai karshen ya na tashi da ga saman sofar ya nufi corridor da kallo Malik ya raka shi har sai da ya shiga sannan ya saki wani dan karamin murmushi ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】 ____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________ PAGE 10 ❤🔥 Amir kuma bayan ya koma bedroom din shi kai tsaye toilet ya nufa jim kadan ya fito sanye da bathrobe da Allamun wanka ya yi ya na fitowa ya nufi dressing room ya shiga ko two minutes ba bai yi ba , ya fito da ga shi sai short , kai tsaye ya nufi katafaren bed din shi ya Haye ya yi rub da ciki , ya kai hannu ya kashe wutar dakin baki daya sannan ya lumshe idanun shi ya dauki wajen good 30 minutes a haka kafin ya jiyo wayar shi ta yi ruri allamun shigowar sako , daman ba barcin ya ke ba da farko har ya so ya share , amma wata zuciyar ta ce ya duba kar a je abu mai mahimanci ne dan karamin tsaki ya ja kafin ya bude idanun shi ya kai hannu ya dauki wayar ya kunna ya kali screen din wata number ce da a ka yi saving da sunnan * MY BELOVED ❤💍* 🤔🤔🤔 ku tsaya beloved ya na nufin masoyina ko na yi batan kai ? tommm wacece wanan beloved kuma 🤔🤔 a hankali ya kai hannu ya cire password din wayar ya shiga wajen Text ya fara karanto sakon ta kamar * Good night yaya Zayd di na ❤😚 * text din ta ba karamin sanyaya mishi zuciya ya yi ba , har sai da lips din shi su ka dan motsa allamun ya so ya yi murmushi amma ya danne a hankali ya fara typing shi ma ya yi mata reply da * Thanks ❤ Good night * ni na zata da ya tura mata zai kashe wayar , kawai sai ya tsaya ya na kallon screen din har sai da ta yi mishi reply kamar haka " Thanks 💋 * reply ya yi mata da * Okay ajiye waya yanzu tafi ki yi barci * ko one minute ba ta yi ba ta yi mishi reply da cewa * kai ma ka tafi ka yi barci 😑 * * shikenan sai da safe * * yaya Zayd gobe za ka zo mu yi breakfast tare ? 🥺🥺 * * eh zan zo * * 🥳🥳🥳 yawwa yaya Zayd ni da kai na zan shirya mana breakfast , na tafi ma dan na samu na tashi da wuri , I LOVE YOU byeeeeee ❤ * * bye * ya na gama rubuta hakan ya kashe wayar ya ajiye saman bedside drawer ya na kallon wayar da allamun ya na jiran sakon ta sannu sannu har barci mai dadi ya dauke shi bai sani ba * WASHE GARI ( misalin karfe 10 ) " Amir ! tashi Ammien ka na son magana da kai " Malik ya fada ya na dan bubuga kafar Amir da ke ta faman sharar barcin shi a hankali ya fara motsi ya na karato adu'ar tashi da ga barci sannan ya ware idanun shi a hankali sai saman Malik da ke tsaye ya tsare shi da wadanan Hazel eyes din na shi cikin magagin barci Amir ya ce " wai malam lafiya ka tashe ni ? " " iyeeeee , lalle idon ka ya bude Amir , yanzu ni ka ke wa wannan tambayar ? Shikenan Tashi ka tafi Ammie din ka ce ke son yin magana da kai , ni zan wuce fada " ya kai karshen ya na juyawa ya fice bedroom din ya na fita Amir ya sauko da kafafun shi kassa ya mike tsaye ya fara takawa ya nufi Toilet jim kadan ya fito daure da towel a kugunshi , ya nufi dressing room kai tsaye nan ma bai wani dauki lokaci ba ya fito sanye da jeans brown color da T-shirt white color , kafafun shi kuma , cikin wasu sneakers farare kal , ya saki wannan smooth hair din na shi , gashin shi yanzu tubarikallah ya toho har ya kai shoulder din shi , sai tashin kamshi ya ke bedside drawer ya nufa ya dauki wayar shi ko duba ta bai yi ba ya saka ta cikin aljihu ya fice dakin ya fito corridor ya shigo parlour , kai tsaye ya nufi lift ya shiga ya sauko kai tsaye ya baro building din ya nufi part din MALIKAT INAS duk inda ya wuce sai dogarai sun sunkuyar da kai su na yi mishi barka da safya in kuma bayi ne , sai sun zube saman guyiwowin su , su na gaishe shi har ya wuce sannan su tashi su ci gaba da tafiyar su shi ko daya bai bi ta kan gaisuwar su ba ya nufi part din MALIKAT INAS , hankalin shi na wata duniyar ji ya ke kamar ya manta da wani abu mai mahimanci a hankali ya motsa lips din shi ya na sallama ya shigo parlourn MALIKAT INAS nan ya tardo ta zaune , ita da RIANNA da Nesrine duk sun yi zugum waje guda su na jiyo sallamar shi su ka dago kai a tare su ka kali saitin kofar su na amsa mishi sallamar shi sannan RIANNA ta daura da cewa " Amir ina ka tsaya wai tun dazu mu na ta kiran ka a waya " karasowa ya yi cikin parlourn ya na fadin " What happening ku ke kira na tun da safe ? " RIANNA na shirin magana MALIKAT INAS ta daga mata hannu ta yi shiru sannan MALIKAT INAS ta ce " Je ka , ka gani da idon ka " ta fada ta na nuna mishi hanyar corridor a hankali ya juya ya kali corridor din sannan ya juyo ya kali MALIKAT INAS ya na son ya yi magana ya shanye ya nufi corridor din kamar yadda ta ce kai tsaye bedroom din Inaya ya nufa a hankali ya sa hannu ya tura kofar ya na sallama cen kassan makoshi ya na shigowa ya gan ta zaune tsakiyar gadon ta juya wa kofar baya ta sunkuyar da kai a hankali ya fara jiyo Muryar ta cen kassa kassa allamun waka ta ke karasowa ya yi cikin dakin ya tsaya dab da gadon ya na rike da hannayan shi a baya murya kassa kassa ya ce mata " Barka da safya " ba tare da ta juyo ba ta ce mishi " barka " a takaice sannan ta ci gaba da wakar ta tsaya wa ya yi ya na kallon ta na wani dan lokaci kafin ya juya a hankali ya fice dakin kai tsaye parlour ya dawo , ya nufi MALIKAT INAS ya tambaye " lafiya wai ku ka kiro ni tun da safe haka ? " cikin bacin rai MALIKAT INAS ta ce mishi " Amir yanzun ne tun da safe , karfe 11 har da mintina ? " shiru ya yi ya tsaya ya na kallon ta , tabbas ta na cikin fushi ba kadan ba , ga Dukkan allamu kuma da shi ta ke fushin cikin nitsuwa ya ce mata " Ammie please calm down , me ya ke faruwa ne ? " nuna mishi Dining room ta yi ta na fadin " tun karfe 6 ta shiga kitchen dan ta shirya maka breakfast , amma ba ka zo ba " Ta na gama rufe bakin ta ta ga juya a hankali ya koma cikin corridor din bedroom din Inaya ya koma shi har ga Allah wlh ya manta da zancen breakfast din da za su yi tare , bare yau wani barci mai dadi ya dauke shi , ba dan Malik ya tashe shi ba da wuya ya tashi yanzu a hankali ya sa hannu ya tura kofar dakin ya shigo ya na sallama cen kassan makoshi ko motsawa ba ta yi ba ta na nan yadda ya bar ta , ta na wakar ta kassa kassa gaban gadon ya karaso ya tsaya kamar dai da farko bai ce mata komai ba ya na kallon ta sai da ya dauki lokaci a haka kafin ya zauna bakin gadon ya kai hannu ya daura saman shoulder din ta ya na fadin " Cutie ! " " uhm " ta fada ba tare da ta juyo ba " ba za ki juyo ba " ya fada ya na janye hannun shi da ga saman shoulder din ta a hankali ta girgiza mishi kai ba tare da ya ce komai ba hannu ya sa ya cire sneakers din kafafun shi sannan ya Haye saman gadon shi ma , ya koma gaban ta su na fuskantar juna ya yi irin zaman cin tuwo shi ma ya na kallon face din ta ya ga uban hawayen da ke konce sama , ga wasu nan na zubawa bibiyu ga shi kuma ba kukan ta ke ba hawayen ne kadai ke zubowa a hankali ya kai ya goge mata hawayen ta ya na fadin " hawayen minene wannan ? " " komai ! " ta fada a takaice ba tare da ta kale shi ba sai da ya gama goge mata hawayen ta sannan ya janye hannun shi ya ce " kin yi breakfast ? " a hankali ta gyada mishi kai allamun eh " yaushe ki ka fara yi min ƙariya " " ni gaskia ce na fada maka , ka tambayi Ammie " " shikenan , minene matsalar to ? " ya fada ya na dan lekon face din ta girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " babu komai " " dago ki kale ni to " ba tare da ta dago kai ba ta ce " yaya Zayd don Allah tashi ka yi tafiyar ka " dan zaro idanu ya yi ya na kallon ya yi mamakin abun da ta fada " kora ta ki ke yi ne ? " ya fada ba ta ce mishi komai ba ta juya ta sauko da kafafun ta kassa ta tashi ta nufi toilet da gudu ta shige ta medo kofar ta rufe ta na shiga ko ta saki kuka mai cin rai har sai da ya jiyo sautin kukan da sauri ya diro da ga saman gadon ya nufi toilet din ya tura kofar ashe ba ta sa key ba ya na shigowa ya tardo ta zaune bakin bath ta sunkuyar da kai ta na kuka nufar ta ya yi bai ce mata komai ba ya sa hannu ya dauke ta cak kamar baby ya juya ya bar toilet din ta na jin ya dauke ta ta fara wuntsila kafafu ta na fadin " yaya Zayd ni ka sauke ni " bai dire ta ko ina ba sai saman bed din ta sannan ya juya ya nufi door ta dauka fita zai yi kafin sai ta ga ya tura kofar ya rufe ya juyo ya dawo cikin dakin ya nufi bed din ta na ganin ya nufo ta , ta yi sauri ta mike zaune ta juya daya geffen ta na shirin sauka kafin ma ta sauko da kafafun ta kassa ya karaso wajen bed din ya riko hannun ta da karfi ya meda ta konta ya Haye saman gadon , ya riko hannayan duka biyu da hannu guda a saman kan ta saman ya sa dayan hannun ya ware kafafun ta ya shiga tsakiya sannan ya kawo face din shi saitin ta ta tsuke gera ta yi ta na fadin " yaya Zayd ka sake ni , na tafi " " yi min shiru , yaushe ki ka fara meda min magana ? " ya fada sam babu wassa a tare da shi turo dan bakin nan nata ta yi ta kauda kai gefe dan ba ta jure kallon cikin idanun shi a hankali ya kai bakin shi saitin kunen ta murya cen kassan makoshi ya ce mata " i'm sorry , ba zan sake ba " ya na gama fadar haka ya ji ta sauke wata nanauyar ajiyar zuciya slowly ya saki hannayan ta sannan ya sauka da ga saman ta , ya koma gefe ya zauna ya na sauka ita ma ta mike zaune ta na sa hannu ta na goge face din ta ta ce " ka san ba za ka zo ba shi ne ka ce min za ka zo , tun safe na ke jiran ka , amma ka manta da ni " " ban manta da ke ba " ya fada ya na riko hannun ta a hankali ta ta fada jikin shi ta rungume shi ta na fadin " ni na ma yi fushi da kai " zagayo da hannayan shi ya yi a bayan ta ya rungume ta shi ma sannan ya ce mata " Shikenan sake ni tun da kin yi fushi , ni ma na yi fushi " yar karamar dariya ta yi ba tare da ta ce komai ba ta lumshe idanun ta a hankali ya yi geffen damar shi ya konta da ita a jikin shi , a hankali ya fara shafa bayan ta ya lumshe idanun shi , shi ma nan take kamar da wassa barci ya dauke su a tare a haka su na manne da juna ▪AFTER SOME HOURS sannu sannu har sai da su ka share wajen good two hours su na barci a haka a hankali Amir ya bude idanun shi ya na karanto kalmar shahada ya na bude idanun shi su ka sauka kan Inaya da ke ta faman barcin ta cikin konciyar hankali a hankali ya zame hannayan shi , ya mike zaune a hankali ya kai hannu ya dauki Sneakers din shi ya saka , sannan ya mike tsaye ya dan juya ya kale ta na dan lokaci kafin ya juya ya fara takawa ya fice dakin , ya na fitowa parlour ya ga babu kowa bai tsaya neman su ba ya sa kafa ya fice part din har ya nufi building din su , wata zuciyar ta ce mishi ya tafi wajen MALIKAT AL'UMU a haka ko ya juya ya nufi part din MALIKAT AL'UMU bakin shi dauke da sallama cen kassan makoshi ya shigo part din a tare Rouksar da Tesnim su ka kai kallon su wajen kofar su na amsa mishi sallamar wani kyawatencen murmushi Rouksar ta saki , ta na shirin yi mishi magana ya riga ta cewa " Tesnim where is mom ? " ya fada ya na kallon Tesnim " ta na wajen Mamie " ta ba shi amsa gyada kan shi ya yi a hankali kafin ya juya ya fara takawa da sauri Rouksar ta mike ta bi bayan shi Tesnim na kallon ta amma ba ta ce mata komai ba har sai da ta fice ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】 ____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________ PAGE 11 ✍📚 ya na tsaka da tafiyar kawai ya jiyo Muryar Rouksar a bayan shi ta na fadin " Amir ! Amir ! " ko juyo wa bai yi ba bare ya amsa ta , har yanzu bai manta abun da ta yi wa Inaya ba , ita ba ta san da ya ga komai ba da sauri ta sha gaban shi ta tare mishi hanya ta na fadin " Amir tun dazu fa na ke biye da kai , ka na ji na ka kyale ni " kallon ta ya yi na dan lokaci kafin ya ce " ban hanya na wuce " ya fada dan ya fi karfin ya raba ta geffen ta dan ya wuce kashe mishi murya ta yi ta na cewa " Akhie ni fa kawai gaishe ka na taho yi , ba na samun damar ganin ka , kuma Tesnim ta ce min za ku yi tafiya ko ban kwana ba mu yi ba " ta kai karshen ta na marairaice murya a hankali ya lumshe idanun shi ya na furza iska da ga bakin shi kafin ya bude idanun shi slowly ya kale ta ya ce " okay ! yanzu zan je na yi sallat , zuwa yamma ki same ni a garden " dan zaro idanu ta yi ta na washe baki ta ce " Da gaske ? " gyada mata kai ya yi kafin ya ce " eh , zan iya wucewa yanzu " da sauri ta koma gefe ta ba shi hanya " thanks " ya fada cen kassan makoshi kafin ya fara takawa ya bar ta nan tsaye tsaya wa ta yi ta na bin shi da kallo har dai ya bacewa ganin ta sannan ta saki wani makirin murmushi ta juya ita ma ta koma part din MALIKAT AL'UMU Shi kuma Amir kai tsaye Part din su ya nufa , bai tsaya ko ina ba sai a floor na uku ya na shigowa parlour ya tardo Diya zaune tare Malik su na hirar su kamar abokan juna Malik na ganin shi ya ce " Amir ina ka shiga kuma ban gan ka a mosque ba yau ? " ko sannu Amir bai ce mishi ba ya nufi corridor ya shige Bedroom din shi ya na shiga Diya ya bushe da dariya ya na fadin " ran ka shi dade , ai ba zai iya fada muku ba , amma ni na san da ga wajen babyn shi ya ke " dan tabe baki Malik ya yi ya na fadin " tooooo , abun haka ne ? amma ka ga dan rainin sens ya ke ce min wai shi ba ya son ta " " Ran ka shi dade wlh ba gaskiya ba ne , Tun lokacin da ya sauke ido saman yarinyar nan ya kamu da son ta tsawon shekara shidda biyar yanzu , ka san yadda Izza ta ke bare ta hadu da Mulki..... " da sauri Diya ya rufe bakin shi ya na dan zaro idanu ya ma manta da wa ya ke magana yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya ce " When LOVE MEETS POWER , ba za ka ji da sauki ba " ya na kai karshen ya na sakin wani cool murmushi dan abun ya tuno mishi tarihin soyayyar shi da MALIKAT INAS , shi ma da farko haka ta dinga yi mishi irin wannan jan aji , ita ga ta daughter din Malik guda ya yi nisa cikin tunanin shi ya jiyo Muryar Diya ya na fadin " har yanzu ya kassa yarda da abun da ke cikin zuciyar shi , amma so dai Amir ya na mutuwar son yarinyar nan , izza ce ta yi mishi yawa ba zai iya bude baki ya ce ya na son ta " " kenan jira ya ke ta ce ta son shi ? " a hankali Diya ya girgiza mishi kai ya na murmushi ya ce " ta jima da ta fada mishi wannan kalmar ta so , amma bai karba " cikin nitsuwa Malik ya katse shi da cewa " nan gaba kadan zai karba , tun da har ya karbe ta a matsayin matar shi ta sunna , kuma ya na son ta cikin zuciyar shi , nan gaba kadan zai bude baki ya furta mata wannan kalmar " " in sha Allah ran ka shi dade , nan gaba kadan za ka fara ganin jikokin ka " yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya ce " haba Diya ina wannan babyn za ta iya daukar Amir , ai shi ya san dalilin da ya sa bai karbi soyayyar ta ba , ba dan ba ya son ta sai dan ya san kan shi , ya san halin kan shi in dai ta wannan fanin ne , ba karamin jarabbabe ba ne , na san haduwa guda za su yi , ku tafi jinyar watanni " dariya sosai Malik da Diya su ka yi a tare , kai gulma dadi 🤣🤣 hayala yau dai Malik da Diya sai da su ka bude wa Amir na shi zaman shi kuma Amir ya na Shiga Bedroom din shi ya wuce kai tsaye cikin toilet jim kadan ya fito daure da towel a kugunshi ya wuce kai tsaye dressing room nan ma bai wani dauki lokaci ba ya fito sanye da wata jallabiya fara kal mai dogayen sai baza kamshi yake ya na fitowa ya nufi wajen da daddumar shi ke shinfide ya Haye ya tada sallar shi cikin nitsuwa bayan ya Kamala ya zauna ya na karatun kur'ani har sai da lokacin sallar la'asar ya zagayo ya tashi ya gabatar da ita bayan ya Kamala ya yi aduo'in shi , ya mike tsaye ya cire jallabiyar jikin shi ya tila ta saman bed din sannan ya nufi bed din ya Haye ya yi rub da ciki , ya lumshe idanun shi , tun da ya dawo cikin masarautar ya ke jin wata muguwar kasala ta rufe shi , ba shi da aikin yi sai barci bari mu leko wani bangaran na cikin masarautar kafin ya tashi * DAMBA zaune ya ke kassan Bishiyar nan dai , kamar kullum yau ma ya na cikin wadanan bakaken kayan na shi , ya rufe fuskar shi da bakin rawani , idanun shi kadai a ke iya gani Rouksar na tsaye a gaban shi ta na fadin " Shirin mu ya fara tafiya yadda ya dace " dan gyada kan shi Damba ya yi kafin ya ce " Tukunna Shirin mu bai fara ba " cikin rudu Rouksar ta ce mishi " Ban gane abun da ka ke nufi ba , a sani na shirin mu shi ne na janyo hankalin Amir gare ni " cikin nitsuwa Damba ya daga mata hannu ya katse ta sannan ya ce " Shiri na daban na ki daban , amma nan gaba za ki sani , ke dai ki yi kokari ki shawo hankalin Amir gare ki , tabass zai bukaci macen da za ta kontar mishi da hankali bayan dawowar shi da ga Makkah " " Ni fa sam ban gane abun da ka ke fada " Rouksar ta fada dan ya na neman ya juya mata shirin da ta yi dangane da Amir wata shegiyar dariya Damba ya yi sannan ya ce " Za ki gani nan gaba kadan " ya na gama fadar haka ya bace bat a wajen ya na barin wajen Rouksar ta saki wani dan karamin tsaki ta na fadin " za ka ga abun da na shirya maka ! " ta na gama fadar haka ta saki wani makirin murmushi sannan ta bace bat ita ma ▪AMIR misalin karfe 8 na yamma su na zaune a cikin dining room din Part din Malik kamar kowa ne dare dan su dining kowa ya nitsu ya na cin abincin shi Amir kuwa ya sunkuyar da kai sai juya spoon din shi ya ke cikin Plate din , da allamun hankalin shi na nesa su na a haka su ka jiyo Muryar Malik ya na fadin " MALIKAT INAS , in sha Allah zuwa gobe za a kai miki kudin da a ke fitar wa sadaka kowace shekara wannan shekarar ke za ki raba " har hada baki MALIKAT INAS da MALIKAT AL'UMU su ke su na fadin " amma ran ka shi dade ba ....... " cikin nitsuwa ya daga musu hannu ya katse su sannan ya nuna Amir ya ce " ku tambaye shi , shi ya bada shawarar " a tare su ka jiyo su ka kali Amir da ke ta faman juya spoon din shi , da allamun ba ya ma tare da su su na ganin hakan kowace ta ja bakin ta , ta yi shiru dan sun san ko sun yi maganar ba zai amsa musu ba haka su ka ci gaba da cin abincin su har sai da su ka Kamala kowa ya tashi ya yi tafiyar shi , Amir kuma ya koma bedroom din shi , da allamun yau na miskilancin su ka mishi busa ▪AFTER SOME DAYS Tun safiya Manya' manyan motoci su ke shigowa Filin Daular da ga Sarakunan masarautun da ke karkashin Daular saudiya har da ahalin Malik da kan shi da mazaunan fadar da ahalin su , kowa zowa ya ke ya na yi wa Malik da Amir Allah kiyaye hanya , ma su yi tsakani da Allah na yi , ma su muguwar manufa a zuciya su ma na nasu Malik kuwa farin ciki ba a magana hakan ba karamin dadi ya yi mishi ba , Musaman ya sanya a ka shirya musu wallima dan tarben baƙin shi ▪MISALIN KARFE 10 NA DARE duk Sarakunan da su ka zo yi wa Su Malik ban kwana kowane ya koma gidan shi , ahalin Malik ne kawai su ka yi saura a wannan lokacin babu kowa cikin parlourn Malik sai Hussein , da Mohammed tare da Ahalin su , Gimbiya Manisha yarinyar MALIKAT Houda matar Hussein sai kuma Gimbiya Aysher Yarinyar MALIKAT Youssra matar Mohammed kowace ta na tare da yarinyar ta guda , da sunnan sun zo yi wa Amir Allah kiyaye hanya yan mata ne biyu ma su jini a jika renon madara da ice cream ga kuma jinin Sarauta , ba laifi duk sun hadu iya hadu ga kyawo Masha Allah Muntaz shi ne sunan ta wajen Gimbiya Manisha , a shekaru za ta kai 24 Haka sannan kuma ta wajen Gimbiya Aysher , Hafsat a shekaru za ta kai 21 years tun da su ka shigo parlourn Malik babu wanda ta ce ma yar uwar ta ufan wai su ji'ji da kai sai tsuke fuska su ke su na shan tsami , su kali nan , su kali nan su na duba Amir , amma ina ko hango Bedroom din shi ba su yi Su na a haka su ka jiyo wani mugun qamshi mai dadi ya daki hancin su , a tare duk su ka kai kallon su wajen da su ka jiyo qamshin sun dauki wajen good on minutes a haka kafin Su ga Amir ya fito da ga cikin Corridor kai a sunkuye ya na latsa wayar shi ya na sanye cikin wasu Tracksuit Farare kal , rigar ta na da hula , an Rubuta NIKE da launin Black da ga gaban ta , kafafun shi kuma cikin wasu sneakers Farare kal su ma abun dai Masha Allah , ya saka hannu guda cikin aljihun rigar sai baza qamshi ya ke kamar wanda ya yi wankan turare kai tsaye ya shigo parlourn babu ko sallama , abun da ba su ni ba ya yi sallama amma shi kadai ya ji abu ne , Idan ba ka kali lips din shi ba da kyau ba za ka ce ya yi sallama ba Muntaz da Hafsat na ganin kowace ta washe baki ta na kara yaba irin wannan kyawon na Amir su na a haka ya zo ya nufi Hanyar fita wajen ko sannu bai ce musu ba da sauri Malik ya taro shi ya na fadin " Amir ba ka ga mutane ba a wajen ? " slowly ya dago kan shi ya kali su Hussein da matan su sannan ya ce musu " Hi ! " da ga haka ya juya ya ci gaba da tafiyar shi " Nawfel ba za ka tsaya ka gaishe da Auntyn ta ka ba ? " Gimbiya Aysher ta fada cike da kissa hmm ni kuma na ce kin yi a banza dan ko kallon inda ta ke bai yi ba ya sa kai ya fice da sauri Hafsat ta mike ta bi bayan shi kamar ko ya san haka za a yi , ya na fitowa ya ce ma Azim kar ya bar kowa ya fito wajen da sunnan zai biyo shi Hafsat na isowa Kofar fita parlourn Azim ya tare ta ya na fadin " yi hakuri ran ki shi dade , Shugaba ya ce kar a bar kowa ya biyo shi " ba dan ta so ba ta koma cike da bacin rai ta zauna kusan mahaifiyar ta ta , ta hura kumatu da iska wai ita ta ji haushi duk abun da ya faru Malik na gani amma bai yi kokarin tsayar da Amir ba , sai da ya fita sannan ya shiga bawa Gimbiya Aysher hakuri ya na cewa wani aiki ne zai je yanzu zai dawo su yi sallama da ga haka su ka ci gaba da hirar su Amir kuwa ya na fitowa kai tsaye part din MALIKAT INAS ya wuce ( hmmm 🤔🤔🤔 ko me ya je yi a cen ) bakin shi dauke da sallama ya shigo parlourn ta , ya nufi Hanyar corridor ko dago kai bai yi ba bare ya san da mutum ko babu har ya ka tsakiyar parlourn ya jiyo Muryar MALIKAT INAS ta na fadin " Amir lafiya dai ko ? ka zo ka wuce ni haka ko sannu babu " a hankali ya tsaya da ga tafiyar shi ba tare da ya dago kai ba ya ce " lafiya Ammie " dan karamin murmushi MALIKAT INAS ta yi kafin ta ce " shikenan zo zauna ina son mu yi magana " a hankali ya dago da kan shi ya kale ta na dan wani lokaci kafin ya juya a hankali ya nufi Sofa ya zauna ya na kallon ta , irin kallon nan na son karin bayani sai da ta dan dauki lokaci kafin ta ce " Amir ni fa ban san yadda a ke raba kudin nan na sadaka ba , ya za ka tashi lokaci guda ka ba ni ya zan yi yanzu " ta fada ta na dan marairaice fuska wani dogon nunfashi ya ja kafin ya ce " Kar ki damu Ammie na san za ki yi abun da ya dace , dalilin da ya sa na ce a ba ki kudin na lura wanda su ka yi sadakar ba sa yin ta tsakani da Allah , kuma ban yarda da zubin su ba gaskia " " to ya ka ke so a yi yanzu dan ni fa ba wani abu da na sani " a hankali ya gyada kan shi kafin ya ce " in sha Allah za ki sani , zan sa a karo miki Four Milliard saboda kudin ba za su isa ba , Five milliards kennan , ina son ki raba kudin nan tsakanin Gidan Marayu , zan sa a fitar da duk wani kayan abinci na cikin Store da ya wuce Two months , za a raba tsakanin Al'uma musaman manoma da kananan yan kasuwa , haka zalika kudin za a raba su tsakanin Manoma har wajen masarautar , su ma bayin da ke cikin masarautar nan a fidda na su rabon , sannan kuma mutanan Gari ma su karancin hali , kar ki manta da gidajen marayu massalatai da public Schools , Ammie dalilin da ya sa na ce a baki kudin ba momy ba saboda na san wacece ke , na san za ki rabon nan yadda ya dace , kar ki damu ita ma momy za a kai mata nata kudin , kuma in sha Allah bisa wannan tsarin za mu ci gaba " " Masha Allah " MALIKAT INAS ta fada cikin zuciyar ta , ta na sakin wani kyawatencen murmushi gaskiya abun da ya fada ba karamin burge ta ya yi ba , tabass ya cika sunan shi na magajin Malik ya na a haka ya juyo Muryar shi ya na fadin " Zan iya tafiya ? " " Ina kuma za ka je " ta fada ta na mishi hararrar wassa cikin ko in kula ya ce mata " wajen matata zan je ko da magana " yar karamar dariya MALIKAT ta yi kafin ta ce " ko daya , yanzu ina uwar gidan ka , za ka tashi ka bar ni ka je wajen Amaryar ka ? " " In kishi ki ke , yanzu za ki fara " ya kai karshen ya na mikewa tsaye dan tabe baki MALIKAT ta yi ta na fadin " yanzu Amir ni za ka fadawa haka , dan ka yi amarya , shi ne za ka manta da uwar gida ? " ko sannu bai ce mata ba ya nufi corridor abun shi da kallo ta raka shi har sai da ya shiga sannan ta yi wata yar karamar dariya ita kadai ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】 ____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________ PAGE 12 ✍📚 Amir kuwa kai tsaye bedroom din Inaya ya nufa bakin shi dauke da sallama ya shigo cikin bedroom din kai a sunkuye sannan ya juya ya rufe kofar , ya danna wani button a jikin kofar ya saka mata security sannan ya juya ya dago kai ya kali cikin dakin dum ya ji gaban shi ya fadi ya zaro idanu ya na kallon ta konce ta ke saman bed din ta , ta juyawa kofar dakin baya ta na sanye da kananan kayan barcin ta pink colour , wando da kadan ya wuce hips din ta , da yar karamar Riga ko cibi ba ta kai ba , ta na da shilalen hannu , sai hanayan Bra din ta da a ke iya gani , a yi mata wasu kitso guda biyu da gashin ta , sun kai mata har tsakiyar baya , ga kugun nan nata a waje ta saka wata yar siririyar sarka A hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya fara takawa ya karaso cikin dakin sannan ya tsaya bakin gadon nan ya ga ashe ba barci ta ke yi ba , ta na rike da wayar ta , ta na kallon pic din shi , tun lokacin da ya ke 20 years , ya yi matukar mamakin yadda a ka yi ta samu wannan pics din amma bai ce mata komai ba ya tsaya ya ci gaba da kallon ta ya na a haka ya ga ta wuce pic din sai saman wani pic din nashi kuma , a wannan ya zaune saman sofa ya daga kai sama saki wani kyawatencen murmushi har wadanan fararen teeth din nashi sun bayana idanun shi na lumshe da allamun ya na tsaka da dariya a ka yi pic din , gaskia pic din ya hadu kamar ba Amir ba dan karamin murmushi ta saki kafin ta ce " Gaskiya yaya Zayd murmushi na yi maka kyau , why ka daina ? " ta na gama rufe bakin ta , ya ce mata " ki na so na yi miki ? " kara fadada murmushin ta ta yi ta na fadin " Eh ina so , amma fara zama tun dazu ka na tsaye saman kai na " dan zaro idanu ya yi ya na fadin " ta ya a ka yi ki ka san ina nan ? " ya fada dan shi duk a tunanin shi ba ta san ya na cikin dakin ba murmushi mai dan sauti ta yi ba tare da ta ce komai ba a hankali ya nufi wajen kafafun ta , ya zauna sannan ya dan sunkuyo ya sa hannu ya cire sneakers din kafafun shi sannan ya dago ya kale ta ya ce " ko za ki iya zama ina son mu yi wata magana " ba musu ta kashe wayar ta , ta ajiye sannan ta mike zaune ta juyo ta kale shi sai da ya ji gaban shi ya fadi da ya ci karo da face din ta gaskiya ba karamin kyau ta kara ba , dama kwana biyu bai saka ta a idanun shi ba , sai ya ga kamar ta sauya mishi lokaci guda bare kuma ta na shan gyara da ga wajen RIANNA da ita kan ta MALIKAT INAS , abun dai Masha Allah har wani haske ta kara ta sha wani kunshi Red color saman Hanyan ta gwanin burgewa kamar na sace ta na gudu ganin yadda ya tsare ta da idanu ya sa ta sakin wani cool murmushi ta ce " yaya Zayd maganar me za mu yi " sai a lokacin ya dawo cikin hayacin shi , a hankali ya dan sunkuyar da kan shi ya kali hanayan ta nan ya ga kunshin da a ka yi mata , an yi mata zanen wasu flowers abun ba karamin burge shi ya yi ba a hankali ya kai hannun shi ya riko nata hannun murya kassa kassa ya ce " wa ya yi miki wannan " yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " Aunty RIANNA ta saka a ka yi mana ni da Nesi " ba ta gama rufe bakin ta ba ta ga ya dago hannun shi a hankali ya kai saitin bakin shi ya manna mata kiss har da lumshe idanun shi ya yi wani cool murmushi ta saki ta na kallon shi sai da ya yi mata kiss sannan ya dago ya kale ta ya ce " gobe za a fara azumi kin sani ko ? " gyada mishi kai ta yi ta na fadin " Eh yaya Zayd na sani " ta kai karshen ta na komawa ta konta ta na fuskantar ceiling " kin san gobe za mu tafi Ko ? " ya fada a hankali ya na kallon cibin ta sai da ta dan dauki lokaci kafin ta ce " na sani yaya Zayd , har na fara kewar ka " ta kai karshen ta na yar karamar dariya a hankali ya dago da hannu shi ya saka dan yatsar shi cikin hudar cibin ta a hankali ta dago kai ta mike zaune ta na lekon cibin nata a tunanin ta wani abu ne a ciki ita ba ta san Amir ya ga abun ya ja hankalin shi janye hannun shi ya yi ya na fadin " ba komai , har yanzu ba ki fada min abun da ki ke so na sayo miki a cen ba " ya fada ya na dago kai ya kali face din ta komawa ta yi ta konta ta , ta kai hannu ta riko chain din kugun ta , ta fara juya ta ta ce " ni yaya Zayd duk abun da ka kawo min ina so , amma ni kai na fi so " ta kai karshen ta na yar karamar dariya ta lumshe idanun ta dan lumshe idanun shi kadan ya yi kamar mai jin barci , yarinyar nan ta na neman ta birkice mishi tunani shi da ya zo yi mata bankwana kadai a hankali ya kai hannu shi ya riko nata ya janye shi gefe ya daura nashi hankali saman flat tunbin ta ya fara shafawa a hankali shi kan shi bai san ya hakan ta faru ba kawai sai jin kan shi ya yi ya kai bakin shi saman cikin ta ya manna mata kiss sannan ya fido tongue din shi ya saka cikin hudar cibin ta a dubu dari Inaya ta bude idanun ta , ta mike zaune Muryar ta har kerma ta ke yi ta na fadin " yaya Zayd me k... " ba ta kai karshen maganar ba ta ji saukar yatsar shi saman lips din ta ya zame tongue din shi , ya dago kai ya kawo face din shi saitin ta ta murya cen kassan makoshi ya ce " kar ki ji tsoro ba abun da zan yi miki " wani cool murmushi ta saki ta na gyada mishi kai a hankali ya zame hannun shi ya na fadin " na yi kewar ki sosai idan na tafi , specially wannan dan bakin tsiwar " ya kai karshen ya na kai yatsa ya shafi lips din ta " da gaske yaya Zayd za ka yi kewa ta " ta fada ta na murmushi a hankali ya gyada mata kai allamun eh nan take idanun ta su ka kawo ruwa da sauri ya girgiza mata kai ya na fadin " please kar ki min kuka , so ki ke na kassa samun nitsuwa " girgiza mishi kai ta yi ta na sakin dan karamin murmushi ta ce " Yaya Zayd ba na son ka tafi ka bar ni , one month ya yi min tsayi dayawa " " i'm sorry ko ni ba na jin tafiyar amma ba yadda zan yi " ya kai karshen ya na daura hannun shi saman kumatun ta a hankali ta gyada mishi kai ta na murmushi ta sannan ta ce " amma za ka dawo ko ? " " of course zan dawo mana , ki kontar da hankalin ki , ki kula min da kan ki kin ji ko ? " gyada mishi kai kawai ta yi ta na murmushi allamun eh " shikenan yanzu close your eyes zan ba ki wani gift din bankwana " yar karamar dariya ta yi kafin ta lumshe idanun ta a hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya matso da face din kusan ta ta har hancin su na gogar na juna a hankali ya daura lips din shi saman nata ya manna mata kiss a dubu dari ta bude idanun ta sai cikin nashi ko ( 🤣🤣🤣🤣 maaaaaaamaaaaaaa ki na ina ? yau Amir na shirin lalata miki yarinya 🤣🤣 ) janye lips din shi ya yi ya na lumshe idanun shi a hankali kamar mai jin barci ya ce " Shikenan ! " a hankali ta girgiza mishi kai ta na kallon cikin idanun shi daga mata gera guda ya yi allamun minene marairaice mishi fuska ta yi ta kassa ce mishi wani abu a hankali ya kai bakin shi saitin kunnen ta ya ce mata " Ki na son wani ? " kamar ya san abun da ta ke son fada mishi a hankali ta gyada mishi kai allamun eh " shikenan rufe idanun ki " ya rada mata a kunne ba musu ta rufe idanun ta , ta sauke ajiyar zuciya ya na jin ta sauke ajiyar zuciya ya lumshe idanun shi ya manna mata kiss a wuya sannan ya dago kan shi ya na kallon face din shi , ya rasa me ya ke ji cikin zuciyar shi a hankali ya zagayo da dannu shi a bayan ta , dayan kuma ya daura saman kumatun ta slowly ya kai bakin saitin nata ya daura lips din shi saman nata kamar dama jira ta ke ya daurawa ta cabko lips din shi na kassa ta tsotsaya kamar ta samu sweet ba shiri Amir ya bude idanun shi , ya na dan zaro su , shi fa ba abun da ya shirya yi ba ne ya na a haka ya ji kawai ta zagayo da hannayan ta a wuyan shi ta mike saman guyiwowin ta ta ci gaba da kissing din cikin kwarewa bawan Allah duk ya bi ya rude ya rasa abun da zai mata , shi ya ma rasa ina ta koyo irin wannan Hot French kiss nan take ya ji duk wata Sigar jikin shi ta mike , duk wasu kofofin Feeling din shi sai da su ka bude su na karbar sakon ta ( 🤣🤣🤣🤣 wayooo yarinyar nan za ta kashe min Amir lokacin shi bai yi ba 🤣🤣🤣🤣 ) ya yi nisa cikin duniyar shi kawai ya ji ta fara shi a hankali ya yi baya ya fadi ta fado saman kirjin shi ba tare da ta zame bakin ta ba " anya ba Aljanu su ka shiga yarinyar nan ba ? " ya fada cikin zuciyar shi ya na kallon yadda ta lumshe idanun ta ta ki yarda ko so guda ta bude su shi ko so ya ke ta bude idanu ya ga shi sai da gasken ita ce ko kuwa an sauya mishi babyn shi a hankali ya ga ta fara bude idanun ta slowly ta na bude su ko sai cikin nashi su ka yi ido hudu dan zaro idanu ta yi ta na kallon shi , ba shiri ta zame bakin ta ta sauka da ga saman shi ta mike zaune ta na fadin " yaya Zayd ka yi hakuri don Allah " ta fada kamar za ta yi kuka har sai da idanun ta su ka ciko da ruwa a hankali ya kai hannu ya riko nata ya janyo ta da karfi ta fado saman Chest din shi har da ta ce " ashhhhhhhh " a hankali dan lumshe idanun shi ya yi kamar mai jin barci ya ce " hakurin me ki ke ba ni " a hankali ta sunkuyar da kai ta lumshe idanun ta murya na kerma ta ce " ba ba ba komai ? " ta na gama fadar haka ta ji ya juya da ita ta koma saman bed din ya yi mata runfa da fafadar kirjin shi slowly ta bude idanun ta ta na kallon shi ta na son ta ce wani abu ta na jin tsoro a haka ta jiyo Muryar shi ya na fadin " can i ? " a hankali ta gyada mishi kai allamun eh duk da ma ba ta san tambayar me ya ke yi mata ba ta na a haka kawai sai ganin ta yi ya sa hannu ya fara yin sama da rigar jikin shi ya cire ta ya ajiye gefe ya bar singlet kawai ya na ajiye tashi ya sa hannu ya fara yin sama da ta ta , ya fida mata ita ya ajiye saman tashi ya bar mata bra din ta dan tsayawa ya yi ya na bin surar jikin ta da kallo ya na kallon wadanan tula tulan nata babu ko kiftawa , a haka ma su na cikin bra , da a fili su ke na san sai ya zauce , sai hadiyar yawu ya ke ya na kallon su ta na shirin tambayar shi me zai yi kawai ta ji saukar lips din shi saman nata , ya fara kissing ta , ya lumshe idanun shi a hankali ya tura tongue din shi cikin bakin ta ya tsabko tongue din ta ya fara sucked kamar ya samu sweet ta na a haka ta ji saukar hannun shi saman kugun ta , ya shafa a hankali kafin ya sa dan yatsa ya fara yi mata tafiyar tsutsa wani irin dogon nunfashi ne ja ta na bankaro mishi kirjin ta kamar dama jira ya ke yi ya kai hannu ya damko boobs din ta da karfi ya matse wani irin Zir ya ji tun da ga tafin kafar shi ya tsakiyar kan shi nan take ya ji dick din shi ta fara yi mishi wani iri tsilo a cikin Short din shi kamar za ta fassa short din ta fito a dubu dari ya zabe bakin shi da ga cikin nata ya na fadin " Ashhhh " da dan karfi ya sauka da ga saman ta ya koma gefe ya konta ya juya mata baya ya lumshe idanun shi ya kankame waje guda nan take duk jikin ya fara rawa ya na kerma kamar mai zazzabi wata nanauyar ajiyar zuciya Inaya ta sauke ta lumshe idanun ta , har ga Allah ta ji zafin matse mata boob da ya yi amma babu bakin magana a lokacin sai da ta dauki good ten minutes idanun ta a lumshe kafin ta bude su slowly ta na kallon ceiling a hankali ta juyo ta kali Amir dum ta ji zuciyar ta ta buga ganin yadda ya ke wannan rawar jiki ga wata uwar zufa da ta karayo me kamar an watsa mishi ruwa da sauri ta mike zaune saman guyiwowin ta , hankali a tashe ta ke fadin " yaya Zayd , me ya same ka ? " a hankali ya juyo ya kale ta , ya dan lumshe idanu ya sake bude a kan ta sannan ya ce " ba komai " nan take idanun ta su ka ciko da ruwa ta na girgiza mishi kai kamar ta yi kuka ta ce " yaya Zayd duba yadda jikin ka ke kerma ka ce min ba komai , bari na je na kira Ammie ta zo ta duba ka " ta kai karshen hawaye na zubo mata ta juya da sauri za ta sauka da ga saman gadon da sauri ya riko hannun ta murya cen kassan makoshi ya ce mata " no ba sai kin kira ta ba " fashewa da kuka ta yi ta na fadin " Yaya Zayd ka bari na kira ta kar wani abu ya same ka " " ba abun da zai same ni , in har ki na tare da ni ki daina kukan nan don Allah ki na kara min ciwo da kukan ki , please ki daina ba na so " ya fada mata cen kassan makoshi kamar an shake shi da sauri ta kai hannayan ta dukka biyu ta fara goge hawayen ta ta na fadin " Shikenan , shikenan na daina , fada min abun da ka ke bukata na kawo maka " ta fada wasu hawayen na zubo mata , tun da ta ke da Amir ba ta taba ganin shi cikin irin wannan halin ba ko lokacin da ya yi doguwar suma ba ta ji irin tsoron da ta ke ji a yanzu ba a hankali ya mika mata hannun shi ba musu ta daura nata saman nashi , ta na daura wa ya janyo ta a hankali ta fado saman kirjin shi , ya zagayo da hannayan shi dukka biyu a bayan ta ya rungume ta tsam a jikin shi ya na rungume ta ya sauke wata nanauyar ajiyar zuciya ya lumshe idanun shi ita kuma ta ida lafewa a jikin shi ta boye fuskar ta a kirjin shi sannu sannu har ya daina Rawar jikin nan da ya ke yi , da ga haka kuma barci barawo ya yi gaba da su , su na manne da juna ( kamar na kwace mishi ita na huta 😑😑😑 ) ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】 ____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________ PAGE 13 ✍📚 ▪MISALIN KARFE 1 NA DARE a hankali ya fara jiyo Wayar shi ta na ringing , ta katse mishi barcin shi me dadi ya na bude idanu shi su ka sauka saman face din ta tsaya wa ya yi ya na bin face din ta da kallo kamar bakuwar shi , har sai da kiran ya tsinke bai sani ba a haka har wani kiran ya sake shigowa a hankali ya dan lumshe idanun shi kafin ya sake bude su kafin ya zame hannayan shi a hankali da ga rungumar da ya yi mata ya sauke kafafun shi kassa ya mike zaune bakin gadon har ya kai hannu zai dauki rigar shi nan ya ga rigar ta a sama , tsaya wa ya yi na dan lokaci ya na kallon rigar kafin ya kai hannu ya dauke ta , sannan ya dauki rigar ta shi ya kai hannu wajen aljihun rigar ya fido wayar shi , ya na kallon Screen din * MY AMMIE ❤ * shi ne sunan da ya bayana a kai a hankali ya kai hannu ya dauki kiran ya kai wayar a kunne ba tare da ya ce komai ba ya na kai wayar a kunne kuma MALIKAT INAS ta ce " Amir ka na ina , tun dazu Malik ke ta kiran layin ka amma ba ka dauka , ka manta da tafiyar ku ko ya ? ya na jiran ka don Allah yi sauri " ta na gama fadar haka ta katse kiran ba tare da ta jira amsar shi ba ya na jin kiran ya katse ya sauko da wayar ya kali screen din nan ya ga wajen 10 miss call da Malik ya yi mishi kashe wayar ya yi sannan ya saka ta cikin aljihun wandon shi sannan ya ninke Rigar Inaya ya saka cikin aljihun shi , sannan ya juyo a hankali ya kale ta ta na konce abin ta , da ga ita sai bra sai dan wandon ta , ta na barcin ta cikin konciyar hankali a hankali ya matso da face din shi saitin ta ta murya kassa kassa ya ce " Zan yi kewar ki sosai My Cutie " ya na gama fadar haka ya kai lips din shi saman forehead din ta ya manna mata kiss sannan ya manna mata kiss saman kumatun ta dukka biyu , sannan ya yi mata saman lips da ga haka ya kai bakin shi saitin kunen ta ya yi mata rada , ni dai ban ji abun da ya fada mata ba Gaskia ya na gama fada ya mike tsaye ya nufi Sneakers din shi ya saka sannan ya nufi Kofar dakin ya danna button din security ya fita sannan kofar ta yi baya kadan hannu ya sa ya ida bude ta sannan ya juya a hankali ya kali Inaya ya ce " Goodbye My Cutie " ya na gama fadar haka ya juya ya sa kafa ya fice dakin ya janyo mata kofar a hankali ya ke tafiya cikin corridor din kai a sunkuye ya na rike da rigar shi ya fito parlour MALIKAT INAS , RIANNA , MALIKAT HOUDA , MALIKAT AL'UMU , TESNIM kai har shi kan shi MALIK ya na tsaye cikin parlourn kowa ya yi zugum waje guda ya na jiran fitowar AMIR su na ganin Fitowar shi a tare su ka tsaya su na bin shi da kallo ya na rike da rigar shi ko dago kai bai yi ba bare ya kale su ya nufi Hanyar fita parlour din sai da ya kai bakin kofar sannan ya tsaya ya meda rigar shi sannan ya ce " za mu iya tafiya ? " ya na gama fadar haka ya sa kafa ya fice parlourn da kallo duk su ka raka shi sai da ya fita sannan RIANNA ta nufi corridor da gudu , dan ba ta yarda da yanayin da ta gan shi , sai da zuciyar ta ta buga da ta gan shi ya fito riga a hannu ya sunkuyar da kai ta na barin wajen Malik shi ba ya nufi hanyar Fita Parlourn cike da bacin rai , tun karfe 1 na dare ya ke faman Kiran Amir yanzu har karfe 2 ko sallama bai tsaya yi wa mutanan wajen ya na fitowa Sai saman wasu manya manyan Motoci ma su nunfashi , kai tsaye motar da Amir ke ciki ya nufa ya na isa guard din da ke tsaron motar ya bude kofar ya shiga AMIR na ciki zaune ya gama bayan shi da kujerar ya daga kai sama ya lumshe idanun shi , a haka ya shiga motar ko sannu bai ce ma Amir ba ya na shiga Guard din nan ya rufe kofar ya nufi motar su da gudu nan take drivers sy ka tada motocin su ka bar masarautar da mugun gudu kamar za su tashi sama bangaran RIANNA kuma ta na shiga corridor ta nufi bedroom din Inaya da gudu Zuciyar ta na duka uku uku da karfi ta tura kofar dakin ta na fadin " Inaya ! " cak ta tsaya bakin kofa ta na kallon Inaya ta na konce tsakiyar bed din ta , da ga ita sai da bra da wandon ta , ga gadon duk a tirje kamar an yi dambe a sama ( 🤣✌ Ke ba ki ga komai ba nan ) wata nanauyar ajiyar zuciya RIANNA ta sauke kafin ta saki wani kyawatencen murmushi sannan ta juya ta fice dakin ta ja mata kofa ▪AMIR sai da su ka fita da ga cikin masarautar sannan Malik ya kali Amir cike da bacin rai ya ce " me ya shige ka ne Nawfel , ka fi kowa sanin Karfe 1 za mu tafi amma duba yanzu karfe uku ban mintina , me ka je yi ne part din MALIKAT INAS ? " a hankali Amir ya sauko da kan shi , ya kontar da shi saman cinyar Malik ba tare da ya bude idanun shi ba nan take jikin Malik ya yi sanyi , ya san duk lokacin da Amir ya kontar da kan shi saman cinyar shi to ba lafiya ba a hankali Malik ya daura hannun shi saman Kan Amir cikin sanyin murya ya ce " Nawfel , me ya faru ne , akwai abun da ka ke damun ka ? " a hankali Amir ya girgiza mishi kai allamun babu komai wani dan karamin murmushi Malik ya yi kafin ya ce " Har ka fara kewar ta ko ? " har ya Girgiza mishi kai da farko sai ya koma ya na gyada mishi kai kara fadada murmushin shi Malik ya yi ba kariya Diya ya yi mishi , tabass Amir ya na matsanincin son Inaya amma ya ki yarda da hakan , Dole ya san yadda zai yi yanzu dan ganin ya yarda da wannan soyayyar da ke cikin zuciyar shi tun kafin ya fara cutuwa a hankali Malik ya sunkuyo da kan shi ya manna mishi kiss a saman forehead sannan ya ce " kar ka damu , idan jirgin mu ya sauka za ka iya kiran ta " a hankali Amir ya bude baki ya ce " Abbi Mara ta ke yi min ciwo ji na ke kamar ta kamawa da wuta " Shiru Malik ya yi ya na kallon shi , shi sai yanzu ya tuno yanayin da ya ga Amir ya fito da ga cikin corridor din nan , ko riga babu a jikin shi Bushewa da dariya Malik ya yi sai yanzu ya gane abun da ya tseda Amir sai da ya tsagaita dariyar shi sannan ya ce " Nawfel bude idanun ka " slowly ya bude idanun shi ya na kallon sama kallon cikin idanun shi Malik ya yi , ya ga sun yi jazir da Allamun har yanzu a hannu ya ke yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya ce mishi "Nawfel , ba dai ɗiyar mutane ka taba ba " dawo da kallon shi Amir ya yi kan Malik ya na fadin " ba matata ba ce ? " dariya sosai Malik ya yi har sai da driver din su ya dan juyo ya kale su , gwanin burgewa tun bayan bacewar Amir bai taba ganin Malik ya yi irin wannan dariyar ba , sai dai ya yi murmushi Sai da ya tsagaita dariyar shi sannan ya ce " Ai dama ban ce ba matar ka ba ce , ni tambayar ka kawai na yi " " Why za ka min irin wannan Tambayar , ko na yi laifi ? " a hankali Malik ya Girgiza mishi kai ya na murmushi ya ce " ko daya , tashi mun iso " ya fada dai'dai lokacin da motocin su ka tsaya a cikin airport ▪INAYA Misalin karfe 4 na safe ta fara kokarin tashi da ga barcin ta a hankali ta ware idanun ta , ta na karanto adu'ar tashi da ga barci Juya wa ta yi ta kali geffen ta amma sai ta ga babu kowa da sauri ta juya daya geffen nan ma ta ga babu kowa da sauri ta mike zaune ta fara bin dakin da kallo ta na fadin " yaya Zayd ? " ba ta gama rufe bakin ta ba ta jiyo karar wayar ta , ta na ringing da sauri ta kai hannu ta dauki wayar , na kallon screen din ta san ba wanda ke da number din ta sai Amir din ta , shi ya sa ba ta tsaya bata lokaci ba ta dauki kiran ta kai wayar a kunnen ta ko sallama ba ta yi ba ta shiga fadin " yaya Zayd ina ka tafi ka barni ? " ta fada kamar za ta yi kuka a daya bangaran kuma , dan lumshe idanun shi kadan Amir ya yi ya na bude su ba karamin dadi ba ya ji cikin zuciyar shi lokacin da ya ji Muryar ta Shiru ya yi bai ce mata komai ba , sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce " Tashi ki je ki yi sahour ina kiran ki an jima " ya na gama fadar haka ya katse kiran ko jiran ta bai yi ba slowly ta sauko da wayar ta na kallon Screen din kamar da ga sama ta jiyo Muryar RIANNA ta na fadin " tashi to mu tafi anjima ya kira ki " a hankali Inaya ta juyo ta kali kofar dakin RIANNA ta na tsaye ta na sakin murmushi , tun lokacin da ta dauki kiran ta ke nan tsaye gyada mata kai Inaya ta yi a hankali kafin ta mike ta nufi RIANNA ita ta manta da babu kaya a jikin ta da sauri RIANNA ta ce mata " ba dai a haka za ki fita ba ? " sai a lokacin Inaya ta kali jikin ta , sai yanzu ta lura babu komai a jikin ta sai dan wandon ta da bra da gudu ta juya ta nufi Dressing room ta shige yar karamar dariya RIANNA ta yi ta na girgiza kan ta kafin ta juya ta fice dakin ta nufi hanyar parlour ta na fitowa MALIKAT INAS ta ce mata " kin tashe ta ? " gyada mata kai RIANNA ta yi ta na karasowa cikin parlourn ta na fadin " an riga ni " ta kai karshen ta na zama a kassa saman carpet ta na zama Inaya ta fito da ga cikin corridor nan ta tardo Su zaune har da Nesrine saman carpet ka kayan sahour nan tsakiyar su a haka Inaya ta karaso ta zauna kusan Nesrine ta na faman murza ido da hannu guda bari na takaice muku labarin , Haka watan Azumi duk ya share Inaya ba ta fito part din MALIKAT INAS ba , da ga Parlour sai bedroom , kullum ta na cikin daki da ga barci sai Sallat da karatun kur'ani , in dare kuma ya yi Amir ya kira ta , tai ta yi mishi zuba ya na sauraron ta , har barci ya dauke ta ba ta sani ba ranar da a ka fara azumi MALIKAT INAS ta fitar da kayan sadaka duk yadda Amir ya fada mata hakan ta yi ko , MALIKAT AL'UMU ma ba baya ba tun Ranar da Aysher da Hafsat su ka shigo masarautar ba su sake fita ba , ko wace ta na wajen kakar ta wai da sunnan sun zo wajen Amir , mutumin da ba ma ya cikin masarautar bangaran Amir kuwa ya na sha tsokana wajen Malik , har wata yar rama ya yi duk cikin rashin Inayar shi bawan Allah har ya ban tausayi ▪AFTER ONE MONTH kwana biyu bayan Sallar Azumi Amir da Malik su ka fara shirye shiryen dawowa Daular Saudiya , a ranar kuma wani mugun Abu ya faru da su ▪INAYA a hankali ta fito da ga cikin corridor , ta na sanye da wata Abaya Black color mai mugun kyau , babu veil a kan ta , ta saki wannan lalawsan gashin kan shi ta na shigowa ko Azim ya shigo parlourn ya na Sallama da sauri ya nufi gaban MALIKAT INAS ya Zube saman guyiwowin shi , murya na kerma ya ce mata " Gaisuwa na ke ran ki shi dade , Amir na bukatar ganin ku da gagawa a fada " kallon juna su ka yi MALIKAT INAS da RIANNA su ka yi cikin rudu MALIKAT INAS ta ce " Amir har ya dawo ? " " eh ranki shi dade , kuma ya na bukatar ganin ku a fada yanzun nan , tare da AMIRA RIANNA " gyada kan ta a hankali RIANNA ta yi kafin ta ce " Za ka iya tafiya , mu na nan zuwa " ta na gama fadar haka ta ga Azim ya mike da gudu ya juya ya fice parlourn mikewa tsaye RIANNA ta yi ta na fadin " mu je ko Ammie , Baby ki jira mu ina zuwa kin ji ko ? " da to Inaya ta amsa mata kafin ta juya ta koma cikin corridor ta koma bedroom din ta ta na komawa MALIKAT INAS ta mike ta bi bayan RIANNA su ka fice part din baki daya kai tsaye babbar Fada su ka nufa tun da su ka karaso bakin kofar Fadar , su ne jin koke² , da muryoyi su na tashi a dubu dari RIANNA ta shiga fadar babu ko sallama ta na shiga ko sai saman , Gawar Malik konce Tsakiyar Fadar , an rufe shi da wani Farin Tissu ga Amir tsaye Bayan shi ya zuba mishi ido , ya na rike da hannayan shi a baya wata irin razananiyar kara ce RIANNA ta saki ta nufi Gawar Malik , kafin ma ta karaso wajen gawar ta silale a kassa sumamiya MALIKAT INAS kuwa ta yi sumar tsaye ta tsare gawar Malik da ido babu ko kiftawa ga MALIKAT AL'UMU da gefe guda ita ma ta yi Zugum TESNIM kuwa Rouksar na rungume da ita sai kuka ta ke yi MALIKAT HOUDA , MALIKAT DJAOUDATT da MALIKAT YOUSSRA suma su na gefe guda sun yi zugum , ba me cewa komai Su na a haka Amir ya bude baki murya a shaƙe ya ce " Azim , kun san abun da za ku yi , General ina son ganin ka ! " ya na gama fadar haka Ya daga kafa ya raba ta geffen Malik ya fice fadar ya bar su nan ya na fita General ya mike da sauri ya bi bayan shi su na fita Mohammed Sarkin bayi ya ce " Azim ku fara shiri mu kai shi gidan shi na karshe , Allah ya jikan shi ya yi mishi rahama , su kuma wanda su ka yi hakan Allah ya bayanar da su " ya kai karshen hawaye na zubo mishi har da sa rigar shi ya rufe fuskar shi amma ta ciki na ciki , ba shi daya ba , duk rabin su ▪AMIR ya na barin wajen Kai tsaye Part din shi ya nufa ya na isa ya haye floor na uku , ya na shiga ya tsaya a parlour ya bawa kofar baya ya rike hannayan shi a baya ya na tsaye General ya shigo , cikin girmamawa ya karaso bayan shi kadan ya tsaya ba tare da ya ce komai ba sai da Amir ya dan dauki lokaci kafin ya ce " ina son ka fara bincike a kan abun da ya faru , ina son ka kamo ko wanene ya yi harbin nan " dan sunkuyar da kai Amir ya yi kafin ya ce " an gama ran ka shi dade , in sha Allah bayan jana'izar Malik za mu fara bincike a kai " gyada kan shi kawai Amir ya yi ba tare da ya ce komai ba A hankali General ya juya har ya yi taku hudu ya tsaya ya juyo a hankali ya ce " ran ka shi dade mu je ko ? " ba tare da ya juyo ba ya ce " Za ka iya tafiya " tsaya wa General ya yi ya kale shi ba dan lokaci kafin ya juya ya ficewar shi ya na barin wajen Amir ya fara takawa ya nufi corridor ya shige abun shi a haka a ka jana'izar Malik , a ka yi mishi wanka a ka kai shi gidan shi na karshe , duk wani Na cikin masarautar idan ya rasu akwai cemetery a bayan masarautar nan a ke bisine shi , haka zalika shi ma Malik amma abun mamaki Ko hanyar Amir bai leko ba , kowa sai dai ya halarta ban da Amir bayan Jana'izar Malik , Duk wani wanda ke cikin Fada sai da ya nufi part din Amir dan jin dalilin da ya hana shi zuwa Amma tun da ga floor na farko a ka tsaida su , da cewa Amir ya ce kar a bar kowa ya shigo ko da MALIKAT AL'UMU ce da kan ta 😭😭😭DAMA HAKAN YA KE GUDU , GA SHI KUMA SUN RABA SHI DA MAHAIFINSHI , DOLE YA CE BA YA SON GANIN KOWA , 😭😭 NI YANZU TAMBAYAR ITA CE WA YA YI WA MALIK WANNAN AIKIN , DUK YADDA A KA YI WANDA YA YI HAKAN YA NA SANE DA TAFIYAR SU MALIK MAKKAH , DA KUMA RANAR DAWOWAR SU , DAN DA GA GANI MUTUWAR MALIK A SHIRYE TA KE TUN KAFIN SU TAFI 😭😭✌ NI DAI NA TAFI NA YI RARRASHIN AMIR DIN MU [21/09 à 19:00] +234 913 527 7685: ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】 ____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________ PAGE 14 ✍📚 bangaran Amir kuwa ya na shiga kai tsaye bedroom din shi ya wuce ya shiga Toilet ya yi Wanka ya yo Alwalla sannan ya fito ya wuce dressing room jim kadan ya fito sanye da wata Jallabiya Fara kal mai mugun kyau ya sako wannan Smooth hair din na shi , yanzu tsawon shi ya fi na farko , ya zubo mishi saman shoulder har zuwa kirji , sai tashin kamshi ya ke yi ya na fitowa kai tsaye ya nufi daddumar shi ya tada Sallat , ko da ya Kamala bai tashi da ga saman daddumar ba , sai da ya zauna ya dinga jero wa Malik aduo'i , sannan ya dauki alwashin ba zai zubar da kwalla daya ba har sai ya ga bayan wanda ya kashe mishi mahaifin shi , kuma ya san dole a cikin masarautar ya ke amma ba zai iya fadin wanene ba ▪INAYA bayan ta koma bedroom din ta , kai tsaye ta haye bed din ta , ko minti biyu ba ta yi ba , barci ya yi gaba da ita ba ta farka ba , sai Wajen sallar magriba , ko da ta tashi , ta shiga toilet ta yi wanka ta yi Alwalla sannan ta fito ta shiga dressing room jim kadan ta fito sanye da wata dankareriar Abaya Fara kal mai mugun kyau , ta yi Rowling veil din ta a kai sai tashin kamshi ta ke kamar wanda ta fito da ga cikin kwalbar perfume ta na fitowa kai tsaye ta nufi daddumar ta , ta fara gabatar da sallar ta ko da ta Kamala ba ta tashi ba , sai da ta tsaya karatun kur'ani har lokacin sallar isha ya zagayo ta tashi ta gabatar da ita bayan ta Kamala ta tashi ta fito dakin ko da shigo corridor ta tardo RIANNA zaune saman carpet ta kontar da kan ta saman Cinyar MALIKAT INAS da ke zaune saman Sofa ta jingina bayan ta a jikin sofar ta daga kai ta kurewa waje guda ido ga busashun hawaye nan konce saman face din su baki daya karasowa wajen Inaya ta yi ta na fadin " Aunty RIANNA me ya faru da ke haka ? " ta fada dai'dai lokacin da ta ke zama gaban ta saman carpet ita ma a hankali RIANNA ta dago kan ta , ta riko hannun Inaya ta ce " Baby tashi ki je wajen mijin ki , zai bukaci kulawar ki a wannan lokacin , ki tsaya ki kula da shi yadda ya dace , na san yanzu ya na cikin damuwa , ganin ki zai sa ya rage radadin da ya ke ji kin ji ko ? " gyada mata kai Inaya ta yi ta na fadin " shikenan Aunty RIANNA , amma ba ki fada min abun da ke damun ki ba , ga hawaye nan konce saman fuskar ki , Ammie ku ma ga hawaye nan saman Fuskar ku " ta fada ta na dawo da kallon ta kan MALIKAT INAS sai a lokacin MALIKAT INAS ta dawo cikin hayacin ta , a hankali ta juyo ta kali Inaya cikin disashashiyar Muryar ta , ta ce " ba komai baby , tashi ki je wajen Mijin ki , ya fi bukatar ki fiye da mu " da to Inaya ta amsa musu sannan ta tashi ta nufi kofar fita parlourn zuciyar duk ba dadi ganin yanayin da su RIANNA ke ciki a haka ta fito part din ta nufi Building din Amir , duk da so guda ta taba tafiya , amma ta san hanya ta kuma san yadda za ta yi ta shiga abun mamaki kuma ta na zuwa guards din da ke tsarin wajen ko tare ta ba su yi ba a haka ta shiga building din , kai tsaye ta shiga lift ta nufi floor na uku zuciyar ta na duka uku uku bakin ta dauke da sallama ta shigo parlourn nan ta tardo Rouksar , Aysher da Hafsat duk tsaye cikin parlour , Azim ya tare musu hanyar shiga corridor A hankali Inaya ta karaso wajen ta tsaya ta na bin su da kallo ta na so ta tambayi abun da ke faruwa amma sam ba su ba ta fuska ba asali ma kowa ce sai kallon wulakanci ke yi wa Inaya kallon Azim ta yi ta ce " Uncle , yaya Zayd ya na nan ? " dan karamin murmushi Azim ya yi kafin ya gyada mata kai ya ba ta hanya Sannan ya fada mata a wane bedroom za ta same shi a hankali ta daga kafa ta wuce ta na tafiya kamar wadda a ka zarewa lakar jiki Aysher na ganin Inaya ta wuce ta sa hannayan ta dukka biyu ta ture Azim gefe ta na fadin " fin mu ta yi da za ka ba ta hanya ta wuce , ba abun da zai hana ni ganin Amir " ta fada ta na wucewa da sauri Rouksar da Hafsat su ka bi bayan ta har su ka kamo Inaya su ka wuce ta , su ka nufi Bedroom din Amir babu ko Sallama su ka fado mishi a tare Amir kuwa ya na konce bakin gadon shi , ya sauko da kafafun shi kassa da sauri Rouksar ta karaso tsakiyar dakin ta marairaice murya ta ce " Akhie ! " slowly ya bude idanun shi ya mike zaune ya dan lumshe idanun shi kadan kamar mai maye , ga gashin nan na shi ya zubo mishi har saman kirji , dukkan su sai da su ka hadiye yawu ba karamin kyau ya yi musu ba har Rouksar ta bude baki za ta yi magana ya daga mata hannu allamun ta yi shiru ba musu ko ta yi shiru ta tsaya ta na kallon shi , ta na kara yabawa kyawo irin na Amir , ni ta ke kamar ta hadiye shi a hankali ya yi kassa da hannun shi dai'dai lokacin da Inaya ta shigo cikin dakin ta na sallama da wannan siririyar murya ta ta ya na jin muryar ta ya ji wani mugun sanyi lokaci guda , har sai da ya dan lumshe idanun shi ya sake bude su a hankali kafin ya juya ya kale ta , ta na ganin ya kale ta , ta sakin mishi wani cool murmushi cike da shauƙi ya na juyawa ko Azim shi ma ya shigo cikin dakin da sauri , ya na yin karo da idanun ya sha jinin jikin shi tun kafin ya yi magana Amir ya riga shi cewa " Me na fada maka ? " ya fada cikin wata murya cen kassan makoshi kamar an busa sarewa dan dadi , har sai da Rouksar ta dan lumshe idanun ta a hankali cikin zuciyar ta ta na fadin " Masha Allah , ya Allah na roke ka , ka sa ya zama nawa " ta kai karshen ta na bude idanun ta jikin Azim har kerma ya fara yi , ya na fadin " ina neman Afuwa ran ka shi dade wlh sun matsa ne sai s...." cikin nitsuwa Amir ya katse shi da cewa " ku fita ku ban waje ba na son ganin kowa " ya kai karshen ya na sunkuyar da kan shi Inaya na jin abun da ya fada ta dan sunkuyar da kai ta juya za ta fice kamar da ga sama ta jiyo Muryar shi ya na fadin " Cutie ban da ke " ya fada da hausa dan ya san ita kadai ke jin hausa wani cool murmushi ta saki kafin ta juyo ta tako a hankali ta karaso geffen Rouksar ta tsaya ta na kallon shi ta na tsayawa Azim ya ce ma su Hafsat su fita , ba musu su ka juya su ka fice kowace ta na cika ta na batsewa riko hannun Inaya Rouksar ta yi , ta na fadin " wuce mu tafi ke kuma ya ce ba ya son ganin kowa " ba ta kai ga rufe bakin ta ba ta jiyo Muryar shi ya na fadin " sake hannun ta ki fice min da ga nan " dan zaro idanu Rouksar ta yi ta na sakin baki har da cewa " Amir kai fa ka ce ba ka son ganin k....." a dubu dari ya dago kai ya daka mata wata gigitaciyar tsawa ya na fadin " I say get out , Azim duk wanda ya sake shigowa ko da parlour ne sai na ɗaure ka da kai na " nan take idanun shi su ka koma jazir , duk jiyojin jikin shi sai da su ka fito baro baro ba shiri Rouksar ta saki hannun Inaya ta juya da gudu ta bar Bedroom din Azim na biye da bayan ta da gudu dan shi kan shi ya ji tsoron irin wannan tsawar da Amir Rouksar kuma ta na baro wajen kai tsaye lift ta nufa ta shiga kofar lift din na rufewa ta bace bat a cikin lift din Amir kuwa ya na ganin sun bar wajen , ya kai hannu wajen bedside drawer ya dauki wata remote ya danna wasu button sannan ya ajiye ta ya na ajiye ta , kofar dakin ta koma da kan ta ta rufe kan ta , ta saka security sai da ya kofar ta rufe sannan ya juyo ya kali Inaya da ta yi sumar tsaye tun lokacin da ya yi tsawar nan daga mata gera guda ya yi allamun minene ? a hankali ta gyada mishi kai allamun ba komai ba tare da ta ce komai ba ya na ganin hakan ya dan sunkuyar da kan shi ya dafe shi da hannu guda ya lumshe idanun shi dan lumshe idanun ta ita ma ta yi a hankali ta sauke ajiyar zuciya sannan ta bude su a hankali ta fara takawa , ta karaso bakin gadon ta cire flat shoes din ta ta haye gadon ta koma bayan shi ta yi kneel down , sannan ta kai hannayan ta a hankali bayan wuyan shi ta fara yi mishi Taussa dan a tunanin gajiya ce kawai ya ke fama da ita kamar ko ta san ya na da bukatar hakan , a hankali ya fara dago da kan shi ya gyara zaman shi , ta na ci gaba da yi mishi taussar har wata ajiyar zuciya ya sauke ta na jin ya sauke ajiyar zuciya ta saki wani dan karamin murmushi mai sauti sannan ta zagayo da hannayan ta , ta rungume shi ta baya ta kontar da kan ta saman shoulder din shi cikin shagwaba ta na fadin " baby na yi kewar ka sosai fa , shi ne ka dawo ko nema ta ba ka yi ba , ba ka yi kewa ta ba kenan " a hankali ya sa hannayan shi ya cire nata ya juyo ya kale ta ya ce " na yi miki kama da baby ? " turo dan bakin nan nata ta yi ta sunkuyar da kai ta riko gudan hannun Abayar ta , cike da shagwaba ta ce " ni fa ba wancen babyn ba na ke nufi , dama Aunty RIANNA ce ta ce na daina kiran ka da yaya Zayd , wai na dinga kiran ka da Baby ko sweetheart , shi ne kawai na yi " ta kai karshen ta na gyara zaman ta saman gadon ta kauda kai gefe shi kan shi bai san abun da ya ke ji cikin zuciyar shi ba , kawai sai ya tsaya ya na kallon ta slowly ta juyo ta kaleshi ta ce " yawwa Baby , ka san abun da ke damun Aunty RIANNA da Ammie , na ga har kuka su ka yi da na tambaye su me ya faru shi ne su ka ce min wai na taho wajen ka " ta kai karshen ta na hura kumatu ta da iska slowly ya juya da kan shi , cen kassan makoshi ya ce mata " kar ki damu ba komai " daga kafadun ta ta yi kafin ta mike saman guyiwowin ta , ta dawo bayan shi ta tsaya ta sa hannu ta tataro gashin kan shi dukka ta riko cikin hannun ta , ta na fadin " laaaa Baby wannan dukka gashin ka ne , Har ma ya fi nawa yawa " ta kai karshen ta na yar karamar dariya da ga haka ta ɗaure mishi gashin a baya sannan ta konto da kan ta saman shoulder din shi ta ce " amma baby ka sha azumi ko ? , dubi har wata kiba ka yi " slowly ya juyo da kan shi ya kale ta , sai murmushi ta ke saki ya ce " ba ki sha Azumi ko guda ba ke ma , amma kin yi kiba , to ni ma ban sha ko guda ba , kawai dan kin yi kwana biyu ba ki gan ni ba ne " ya kai karshen ya na juya kan shi yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " wa ya ce maka ban sha Azumi ko guda ba , har guda hudu na sha " Ba tare da ya juyo ba ya ce " uhm , me ya sa , kuma Ammie na ganin ki ba ta ce komai ba ? za ta bari ki sha har azumi Hudu , ki shirya to gobe za ki fara ramuwar su " shagwabe fuska ta yi ta na turo dan bakin nan nata ta ce " yo ai ba laifi na ba ne , Aunty RIANNA ta ce wai idan mace na period ko ta yi Azumi ba ya ciki har sai ta Kamala " a dubu dari Amir ya juyo ya kale ta ya na zaro idanu ya ce " Period ki ka fara ? " a hankali ta gyada mishi kai ta na marairaice fuska ta ce " amma Baby da zafi , sai da Aunty RIANNA ta dinga ba ni maganin rage ciwon , sai da na ji kamar zan mutu " ta kai karshen kamar za ta yi kuka ta janye kan ta da ga saman shoulder din shi , ta koma tsakiyar gadon ta zauna ta yi irin zaman cin tuwo ta sunkuyar da kai ta na turo dan bakin nan nata tsaya wa ya yi ya na bin ta da kallo , shi ya sa tun lokacin da ya sauke idanu saman ta ya ji duk ta sauya mishi , ashe babyn shi girma ya yi ba ya nan , ya so a ce lokacin da za ta fara period ya na tare da ita , ya bata kulawar da ta dace da ita har ya bude bakin shi zai magana wayar shi da ke saman bedside drawer ta fara Ringing dan lumshe idanun shi kadan ya yi kafin ya juya ya kai hannu ya dauki wayar , ya dauki kiran ya kai wayar a kunne ya na sallama cen kassan makoshi a daya bangaran kuma amsa mishi sallamar shi Diya ya yi kafin ya ce " Amir ga mu nan ni da Aymane za mu shigo part din ka , amma sun hana mu shiga " " Kai shi wajen RIANNA , Idan na bukaci ganin ka , zan kira ka " ya na gama fadar haka ya katse kiran , ya kashe wayar baki daya sannan ya ajiye saman bedside drawer , dan a yanzu dai ba ya da lokacin kowa sai na babyn shi ya na ajiye wayar shi , ya juya ya kontar da kan shi saman cinyoyin ta , sannan ya ida Hayewa bed din ya lumshe idanun shi yar karamar dariya ta yi kafin ta kai hannu ta fara shafa kan shi ta na fadin " baby ina ganin kamar akwai abun da ke damun ka haka ne ko ? " ta tambaye shi cikin shakku girgiza mata kai ya yi ba tare da ya bude idanun shi ba ya ce " ba na da wata damuwa duk lokacin da ki ke tare da ni " wani kyawatencen murmushi ta saki , kafin ta dan sunkuyo da kan ta , ta kai bakin shi saitin forehead din shi ta manna mishi kiss ta na fadin " Ina son ka sosai da sosai , ka sani ko , ya na yi kewar ka sosai , kullum in na yi sallat sai na roki Allah ya dawo min da kai cikin koshin lafya , yadda za mu tafi shan ice cream " ta kai karshen ta na yar karamar dariya " ba sai mun tafi ba Ice cream din za ta tardo ki inda ki ke " ya fada cikin zuciyar shi ya na kara samun nitsuwa cikin zuciyar shi , ya ji dadi da MALIKAT INAS ta ce ta taho wajen shi , ba kariya ya na bukatar ta a kusa da shi fiye da komai a yanzu , Sautin muryar ta kadai ya isa ya share duk wata damuwar da ke cikin zuciyar shi a hankali ta sunkuyo da kan ta saitin kunnen shi ta rada mishi wani abu kafin ta dago ta na kallon shi ta ce " haka nan ne ko ? " slowly ya bude idanun shi ya na kallon ta ya gyada mata kai a hankali allamun eh yar karamar dariya ta yi , ta na shirin magana ta ga ya mike zaune ya sauko da kafafun shi kassa ya mike tsaye ya ce mata " jira ni ina zuwa " ya na gama fadar haka ya fara takawa ya nufi toilet ya shiga ya rufo kofar da kallo ta raka shi har sai da ya shiga toilet sannan ta juya ta jingina bayan ta a jikin forehead din gadon ta mike kafafun ta , sannan ta kai hannu ta dauko wayar shi saman bedside drawer , ta kunna ta , ta shiga neman game ta fara yi ta dauki wajen Good 30 minutes a haka kafin Amir ya fito ya nufi dressing room ko sani ba ta yi ba jim kadan ta fara jiyo wani qamshi mai mugun dadi dai lokacin da Amir ya fito da ga cikin Dressing room sanye da kayan barcin shi farare kal ma su mugun laushi kamar auduga tun da ya fito ta tsare shi da idanu ba karamin kyau ya yi mata ba , har sai da ya karaso bakin gadon ya Haye shi ma ya zauna su na fuskantar juna ya kai hannu ya kwace wayar shi ya sake kashe ta sannan ya ce " Ba ki jin barci ne ? " girgiza mishi kai ta yi cikin zolaya ta ce mishi " hira na ke da saurayi na " daga mata gera guda ya yi ya na fadin " ina ya ke saurayin ? " " ga shi nan a gaba na " ta fada ta na kashe mishi ido guda maganar ta ba karamar dariya ta so ta ba shi ba , amma sai ya shanye ya bar kayan shi a zuciya dan matso da face din ta ta yi kusan ta shi ta na kallon cikin idanun shi ta ce " baby lafiya ka na min irin wannan kallon ? kar ka cinye ni " [22/09 à 11:13] MEERAH 🪷🩷: ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀 👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑 【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】 Marubuciyar littafin 【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】 【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】 ____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________ PAGE 15 ✍📚 Bai ce mata komai ba , ya sa hannu ya warware veil din ta , ya kai shi wajen face din shi ya shaki qamshin turaren ta , nan take ya ji duk wata sigar jikin shi ta mike nan take wata muguwar Sha'awar ta , ta shigo shi a hankali ya kai veil ya ajiye saman bedside drawer ya na fadin " ba ki jin zafi da wannan abun a kai " girgiza mishi kai ta yi allamun a'a dawo da kallon shi ya yi gare ta ya ce " matso ki ji " ba musu ta matso da face din ta , saitin tashi ta na murmushi a hankali ya lumshe idanun shi kamar mai jin barci , sannan ya sake bude su a kan ta kafin ya matso da face dinshi shi ma har hancin su na gogar na juna , a hankali ya kai bakin shi saman nata ya mata manna mata kiss kafin ya cabko lips din ta na kassa ya fara tsotsaya kamar ya samu sweet ajiyar zuciya ta sauke a hankali ita ma ta lumshe idanun ta , ta na karbar Sakon shi a hankali ya zame bakin shi , ya hade forehead din su ba tare da ya bude idanun shi ba ya ce " i have really missed you " dan karamin murmushi mai dan sauti ta yi mishi idanun ta a lumshe , ita da kan ta ta yi kewar shi sosai musaman wannan dadin da ya fara lassa mata ta na a haka kawai ta ji ya daura hannun saman zip din Abayar ta ya fara yin kassa da shi har sai da ya fida shi baki daya sannan ya sa hannu ya raba ta da abayar jikin ta ya bar ta sai underwear a jikin ta a hankali ya yi kassa da kan shi ya daura shi saman shoulder din ta ya fara yi mata kiss har sai da ya sauko saman tudun boobs din ta wani irin dogon nunfashi ta ja ta yi baya da sauri slowly ya dago kan shi ya kale ta , sai wani lumshe idanun ta ke yi a hankali kamar mai jin barci ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kai hannu ya fida Rigar barcin shi ya ajiye saman Abayar ta da ga haka ya kai hannu shi ya riko kugun ta ya janyo ta , ta fado saman kirjin shi ya sa daya hannun ya raba ta da bra din ta ya ajiye gefe ya na fida mata bra din ko , su ka mike tsatsaye nipples din ta su ka soke shi a kirji da sauri ta sa hannayan ta dukka biyu ta tura shi baya , ta dauki rigar shi ta na boye jikin ta , Muryar ta har kerma ta ke ta ce " Yaya Zayd me ka ke shirin yi haka , ni ka kyale ni " murya a shake ya ce mata " Pl......please ki tsaya ba abun da zan yi miki " rumtse idanun ta yi ta girgiza mishi kai a hankali a hankali ya kai hannun shi ya riko Rigar hannun ta ya ce mata " please cutie , so ki ke yi na...... " da sauri ta kai hannu ta toshe bakin shi , ko jin abun da zai fada ba ta yi ba ta na daura hannun ta ya fudo da tongue din shi ya fara yi mata tafiyar tsutsa saman tafin hannun ta yar karamar dariya ta yi ta na fadin " Ka bari mana " ta kai karshen ta na janye hannun ta ta na janye hannun ta , ya matso da face din shi ya kai bakin shi saitin kunnen ta ya ce " Please Feed me , wlh ina cikin matsananciyar yunwar ki " dan karamin murmushi ta saki kafin ta ce " ba ga ni ba " ta na gama fadar haka ta ji ya sauke lips din ta saman wuyan ta , ya yi mata kiss dan lumshe idanu ta yi , ta na sauke ajiyar zuciya dai'dai lokacin da shi ma ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya kontar da ita saman gadon sannan ya mata runfa da fafadar kirjin shi daga mata gera guda ya yi ya na fadin " lafiya ki na min irin wannan kallon " yar karamar dariya ta yi ta na kauda kai gefe ta ce " ni ba kai na ke kallo ba " " To juyo ki kale ni " ya fada ya na tsare ta da wadanan hazel eyes din na shi sai da ta ida dariyar ta sannan ta juyo da kan ta a hankali , idanun ta ba su sauka ko ina ba sai cikin nashi , sai kawai su ka tsaya su kallon juna cikin ido wani cool murmushi ta sakin mishi ta daga mishi gera guda allamun minene a hankali ya girgiza mata kai ba tare da ya janye idanun shi ba , yau dai ya na son ya ga wannan tsantsar son shi da Diya ke cewa ya na gani cikin idanun ta sai da ya dan dauki lokaci a haka kafin ya sauke wata nanauyar ajiyar zuciya ya lumshe idanun shi jin yadda ya sauke ajiyar zuciya ya sa ta tambayar shi ko lafiya bai ce mata komai ba , kawai ya kai bakin shi saman nata ya fara kissing idanu a lumshe ajiyar zuciya ta sauke kafin ta lumshe idanun ta ita ma ta fara mayar mishi da martani , ta zagayo da hannayan dukka biyu a kugun shi a hankali ya kai hannu shi ya fara yi mata tafiyar tsutsa da yatsar shi , tun da ga saman kugun ta har ya iso saman breast din ta , a hankali ya riko breast din ta da hannu ya fara murza mata a hankali slowly ya zame bakin shi da ga cikin nata , bai sauke shi ko ina ba sai saman nipple din ta , ya fara sucked din ta kamar baby ta na jin saukar lips din shi saman nipple din ta , ta ware idanun ta a dubu dari , a hankali ta kai hannu saman shoulder din shi ta na son ta ture shi amma ina jikin ta duk ba kwari a hankali ta fara sakin mishi kuka , dan fa ya fara yi mata da zafi ba tare da ya sani ba cikin kukan nata ta ke fadin " yaya Zayd ka bari don Allah da zafi " amma ina ko jin ta ba ya yi , da allamun ya fara fita hayacin shi ya na haka kawai ya ji dick din shi ta yi mishi wani tsilo , ba shiri ya zame bakin shi da ga saman nipple din ta ya na fadin " Ashhhhhhhh " da dan karfi , kafin ya fadi a jikin ta ya kontar da kan shi tsakanin shoulder din ta da wuyan ta ya na nunfashi da karfi kamar wanda ya kwana ya na gudu ta na jin ya zame bakin shi , ta sauke ajiyar zuciya ta lumshe idanun ta ▪AFTER SOME MINUTES a hankali ta fara jin wani zafi ya lulube ta , Slowly ta ware idanun ta , ta daura hannun ta saman bayan shi nan ta ji wani mugun Zafi da jikin shi ke yi , kamar wanda ke cikin oven a rudu ta bude baki ta ce " baby Lafiya jikin ka ya yi zafi haka ? " sai a lokacin ya sauke ajiyar zuciya , ya bude idanun shi a hankali sannan rada mata " ba komai " a hankali ta zagayo da dukka hannayan ta a bayan shi ta rungume shi ta ce " kuma jikin ka ya yi zafi haka , ko dai ba ka da lafiya ? " a hankali ya juyo da kan shi ya manna mata kiss saman Kumatun ta ya ce " ba komai kin ji ? " ya na gama fadar haka ya mike a hankali , ya sauka da ga saman ta , ya mike zaune bakin gadon , sannan ya mike tsaye ya nufi toilet da kallo ta raka shi har sai da ya shiga sannan ta kai hannu ta dauki rigar shi saka ta sannan ta koma ta konta ta lumshe idanun ta ta na a haka ya fito da ga cikin toilet ya na sanye da bathrobe , ya wuce dressing room jim kadan ya fito da ga shi sai Short , ya nufi bakin gadon shi ya zauna , ya kai hannu ya kashe wutar dakin , ya kunna bedside lamps sannan ya konta ya na fuskantar ceiling ya lumshe idanun shi , ya daura hannun shi guda saman forehead din shi ▪ROUKSAR tsaye ta ke gaban Damba , sai faman huci ta ke duk cikin bacin rai shi kuma Damba ya na zaune kamar kullum kassan bishiyar shi , ya na kallon ta sai da ta gama hucin ta , sannan ta ce mishi " Damba , yarinyar nan ta na neman ta bata min shiri na wlh " dan lumshe idanun shi kadan ya yi kamar mai jin barci ya ce " Ba abun da za ta yi , Malik ya mutu , ko za ta iya medo shi ? " girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " A'a , amma ai shi Amir ya na raye , kuma na ga allamun shi ma ya fara sake mata , yanzu ya kore mu baki daya da ga part din shi banda ita , har MALIKAT AL'UMU wadda ta haife shi , ya ce ba ya bukatar ganin ta " " yanzu ya ki ke so mu yi a kan ta , wannan yar karamar yarinya ta yi kadan ta ce za ta wargaza shirin da na dauki tsawan shekaru ina yi , rana guda " ya na gama rufe bakin shi Rouksar ta ce mishi " mu kashe ta kawai " " Me ki ke jira ba ki tura mata abubuwan wassan ki ba " hararrar shi ta yi kafin ta ce " Damba , ka daina kiran Babys di na da Abun wassa , ka fi kowa sanin da mun shiga watan Azumi karfin sihiri na , raguwa ya ke kowace rana , har yanzu ba su gama dawowa dai'dai ba , bari ka ga " ta na gama fadar haka ta lumshe idanun ta , ta fara motsa lips din ta kamar ta na magana A hankali jelar gashin ta , ta fara sauyawa ta koma green , fuskar ta , ta fara komawa green ita ma nan take Jelar gashin ta ta fara yin sama , ta na komawa kamar jikin maciji lokaci guda jelar ta zubo ta koma kamar da farko , black color , Fuskar ta ta koma color din ta ta gaskia wani nunfashi mai karfi ta ja kafin ta bude idanun ta , ta na kallon Damba kafin ta yi magana ya riga ta cewa " yanzu ba za mu iya anfani da poison din ki ba ? " girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " No gaskiya sai nan da one month kafin su dawo dai'dai , ko taba skin din ta poison din ya yi , ba za ta yi rai ba " " ba matsala , kafin nan shiri na , na gaba zai fara " cikin rudu ta ce mishi " wane shiri kuma bayan wanda mu ka yi " yar karamar dariya ya yi kafin ya bace bat a wajen ya kyale ta nan tsaye tsayawa ta yi ta na bin bishiyar da kallo , cen kawai sai ta saki wani cool murmushi ta na dan cije lips din ta na kassa kafin ta bace bat ita ma ▪KARFE DAYA NA DARE ▪INAYA a hankali ta ware idanun ta , ta mike zaune bakin gadon ta sauko da kafafun ta kassa , ta mike tsaye , ta fara takawa a hankali ta nufi hanyar toilet ya na jin ta fara takawa ya bude idanun shi dama ba barci ya ke ba a hankali ya dago kai ya na kallon ta , har sai da ta shiga toilet ta medo kofar ta rufe sannan ya meda kan shi , ya lumshe idanun shi jim kadan ta fito da ga cikin toilet din ta dawo wajen gadon ta Haye ta konta , ta juyo ta na kallon shi wani cool murmushi ta saki , kafin ta matso ta kai dan lips din ta , ta manna mishi kiss saman kumatu sannan ta kontar da kan ta saman chest din shi ta na konta wa ko idanun ta su ka sauka saman Dick din shi a hankali ta dago kai ta kali face din shi , ta ga idanun shi a lumshe kamar mai barci mikewa zaune ta yi , ta kai hannu ta riko bakin short din shi ta ɗaga a hankali , ta sunkuyar da kan ta a hankali ta na lekon cikin short din shi , kawai sai ta ga ya na sanye da wani boxer turo dan bakin nan nata ta yi , ta na hura kumatu da iska , ta kai dan yatsar ta a hankali ta riko bakin boxer din ta fara ɗagawa ta yi sama da shi kamar da ga sama ta jiyo Muryar shi ya na fadin " idan ki kuskura ki ka yi min kara a wajen nan , abun da ki ka gani da shi zan rufe bakin ki " Dum ta ji Zuciyar ta ta buga ba shiri ta saki boxer da Short din shi ta na zaro idanu slowly ta juyo ta kali face din shi har yanzu dai idanun shi su a na lumshe ta na tsaka da kallon shi ta ga ya fara kokarin bude idanun shi da sauri ta juya ta konta ta ba shi baya , ta rumtse idanun ta da karfi ta na haka kawai sai jin hannun shi ta yi , ya fara yin sama da rigar jikin ta , har sai da ya fida mata ita sannan ya tila ta cen cikin dakin ya ɗaura hannun shi saman kugun ta , ya janyo ta a hankali ya gama bayan ta da kirjin shi , ya ce mata " ajiya ki ka yi cikin short di na ? " da sauri ta girgiza mishi kai ba tare da ta ce komai ba a hankali ya sunkuyo ya manna mata kiss saman Shoulder din ta sannan ya ce " to me ki ke nema a cikin , in ki ka ga abun da ya ba ki tsoro fa ? " yar karamar dariya ta yi kafin ta ce mishi " ni fa babu abun da zai ba ni tsoro a ciki " " haka za ki ce ? shikenan Tashi ki duba , in ki ka ga abun da ya ba ki tsoro ba ruwana " a hankali ta juyo ta na kallon shi , idanun shi su na lumshe wani cool murmushi ta saki ta na shirin magana ya riga ta cewa " kar ki cika ni da surutu , na san halin ki kamar parrot ki ke " yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " ni fa ba ni da surutu , hira na ke maka " " Wai ke ba ki ga dare ya yi , konta ki yi barci " a hankali ta girgiza mishi kai ta ce " kai ma konta ka yi barci " gyada mata kai kawai ya yi , ya sa hannu ya kara janyo ta jikin shi ya ce " sai da safe " Murmushi ta yi kafin ta ce " Sai da Safe baby , I love you " ta kai karshen ta na lumshe idanun ta sai a lokacin ya bude idanun shi slowly ya kali face din ta , ta lumshe idanun ta ta saki wani cool murmushi ajiyar zuciya ya sauke kafin ya sa hannu ya raba ta da bra din ta , sannan ya manna mata kiss saman forehead din , ya kara matse ta a jikin shi duk abun da ya ke ta na jin shi amma ta kyale , a haka har barci ya dauke ta a jikin shi shi kuma ya lumshe idanun shi kamar mai barci amma ba barci ba ya ke ▪WASHE GARI ( karfe 4 na safe ) a hankali ya fito da ga dressing room ya na sanye da Jallabiya Fara kal mai dogayen hannu Bakin gadon ya nufa ya zauna ya kai hannu ya dan bugi face din ta ya ce " Cutie , tashi lokacin Sallat ya yi " ya na gama fadar haka ya ga ta saki wani cool murmushi , ta bude idanun sai cikin nashi matse gera ya yi ya ce " Kennan ki na farke ma " yar karamar dariya ta yi ta na fadin " jira na ke ka tashe ni " ta kai karshen ta na mikewa Zaune da sauri ya kauda kai gefe ya na mikewa tsaye ya juya mata baya ya ce " tashi ki je ki yi wanka , ki yi sallat " ya kai karshen ya na fara takawa ya nufi kofar fita dakin har ya kai bakin kofar ya jiyo Muryar ta ta na fadin " Baby kayan da zan saka ? " a hankali ya juya ya nufi dressing room jim kadan ya fito , ya na rike da wani box fari , ta na tsaye tsakiyar dakin , ta na sanye da rigar shi gaban ta ya karaso ya tsaya ya mika mata Box din , ta sa hannu ta karba sannan ya juya ya nufi kofar fita dakin ya fice da kallo ta raka shi har sai da ya fita sannan ta ajiye box din saman bed , ta juya ta nufi toilet ta shiga ▪AFTER SOME HOURS ▪AMIR Zaune ya ke cikin parlourn shi , yau dai saman Kujerar gold din Malik ya ke zaune , ya na sanye da Trouser Black color , ta T-shirt Sky blue ya ɗaure wannan smooth hair din nashi a baya , ya dan lumshe idanun shi kamar mai jin barci cen na hango Diya zaune saman sofa geffen shi Wani kyakyawan Saurayi ya na zaune kamanin shi sak da Diya , sai dai wannan ya tara gashin kai sosai , a shekaru zai kai 37 years haka dan da ga gani ba na yau ba ne , ya na sanye da trouser White color da t-shirt Red color sannan General na zaune saman Sofa one seater dayan geffen Amir da allamun wata hirar su ke mai mahimanci su na a haka na ga General ya mike ya sara wa Amir sannan ya juya ya nufi hanyar fita ya bar wajen ya na barin wajen Diya ya ce " Amir , ban ji dadin abun da ka yi ba gaskiya , yanzu ....... " cikin nitsuwa Amir ya katse shi da cewa " Diya ba ka san dalili na na yin haka ba , please bar min wannan zancen " gyada kan shi Diya ya yi a hankali kafin ya ce " okay , bari na gabatar maka da babban yayan mu , Aymane bin Abdoul Mujeeb " ya na gama fadar haka Aymane ya dan sunkuyar da kai ya gaishe da Amir cikin girmamawa , sannan ya shiga yi mishi ta'aziyar Rasuwar Malik gyada kan shi kawai Amir ya yi sannan ya ce " kai ne wanda ya nemi auren AMIRA RIANNA ? " dan karamin murmushi Aymane ya yi kafin ya ce " Eh ni ne ran ka shi dade , ina fatan an karbi bukata ta " " Ba ni da ikon ba ka auren ta , ko akasin hakan , ka fara tambayar ta , idan ta amince fine " yar karamar Diya ya yi ya kai hannu ya dan bugi Bayan Aymane ya na fadin " In kuma ta ki sai a ci gaba da cin gwaurancin da shan lemun tsami " juyowa Aymane ya yi ya harare shi ya ce " za mu koma gida ai " " wa ni ? ai na zo kenan da ga nan wajen baby na na yi , yawwa Amir , wai ina Babyn malam , tun kafin a fara Azumi a ban gan ta ba " ya kai karshen ya na meda kallon shi kan Amir shiru ya yi bai ce mishi komai ba ya dai tsare shi da wadanan hazel eyes din na shi Kamar da ga sama su ka jiyo Muryar Inaya ta na fadin " babyyyyyyy "