💫 KYAWUNA JARABTA TA💫 ✍️M SHAKUR DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAIJINKAI. LITTAFIN NAN NAKUDI NE BUT FOR NOW INA FREE PAGE SO U ALL CAN SHARE. subscription is 500 idan kinaso kibiya nasaki a group zaki turo 500 into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting. S-SQAURE FASHION AND MORE GIDANE NA HIJABAI DA HADADDUN DOGAYEN RIGUNA NA DINKAWA, KUNSAN MA MENENE TANA WANI PROMO NA FREE DELIVERY KOWANI GARI KIKE IDAN KIKASAI KAYANSU ZATA AIKOMIKI DA KAYAN KYAUTA, DON MAGANA DA ITA KO CHATTING NATA UP DAN SAYAN KAYAYYAKIN SU CLICK ON THIS LINK wa.me/+2347030037697 Free page EPISODE 1️⃣ Tudun Yola, Kano! Baban Anguwace kuma sabuwa dan babu mutane haka sosai a anguwan, saidai irinsu uncompleted building da ake kan ginawa dakuma sababbin gidaje da ba'a dade da tarewa cikiba. Baban gidane dayasha fenti milk color, kana ganin ginin gidan kaga ginin irin family house dinan, tsakar gidan mai bala'in fadi, ga katuwar bishiyan mangwaro a tsakar gidan datai y'ay'a sosai dudda basu nunaba, flat biyune agidan wani babban dankareren flat saikuma wani karamin flat mai kamada boys quarters agefenshi, gidan kana ganinshi kasan bawani gidan mai bala'in kudi bane gidan rufin asiri ne dai namai karfi daidai, motoci biyune parke atsakar gidan wata bus mai kyan gaske milk color saikuma mota sienna ash da mai gadi ke wankewa ga dukkan alamu motar maigida ne sabida yanda ya kuke yana wanketa yanabin wakan sangaya dake tashi a karamin radio daya ijiye kan plastic chair. Bude kofar karamin flat din dake kusada babban flat din akayi, wani Matashi ne baki dogo baida jiki sosai yana sanye da jallabiya brown hannunshi rikeda makullin mota yafito, takalmi yasaka sanan yasauko daga matattakalan bakin kofarsu yadumfaro babban flat din, da sallama yabude kofa ya shiga ciki. Babban falo dakeda girman gaske, wani Babban Magidanci ne zaune akan kujera akalla zaiyi 60years kokuma 59, kana ganinshi kaga mai gidan, bakine yanada jiki, hannunshi rikeda jarida dayake budewa yana karantawa. gefenshi kuma wata Mata ce mai kiba Hajiya Balaraba akalla zatai 40yrs tasaka wani hadadden lace tana kurban shayi a cup, saiga yara dasuke zazzaune akasan carpet suna breakfast kowanne nashan tea da bread da soyayyan egg dinshi, Mata uku ne a tsakar falon da maza biyu wanda duk kasansu daya, Amal that is 14, sai Asiya 13yrs, sai Aneela dakenan 11, Mazan kuma Muhammad dakenan 11 sai Mudasir wanda shine autan gidan 6yrs, gabaki dayan yaran kana ganinsu kaga mahaifinsu tundaga bakin fatar da jikin dan dukansu tuluka tuluka dasu very fat gwanin ban sha'awa kana ganinsu kasan sunacin lafiyayyen abinci, dukansu suna sanyeda uniform din makaranta da alamu hadda zasu danyau sunday. Kitchen aka bude, wata black beauty Matace dan itama ba yarinya bace akalla zatai 38yrs tafito tana sanyeda doguwan rigan atampa mai kyau da akama stonework tana rikeda tray dawasu hadaddun kwanuka ke kai, hada ido tayi da wanda ya shigo dakin dukbasu luradashi ba yasa tace "this children zasusa kayi latti for your program Ya Hamad" kiran sunan shi datayi yasa duka yaran dakowama na falo yadagokai ya kallai, atare duka yaran suka gaidashi "Ya Hamad good morning" batare daya amsasu ba yakarasa shiga falon har gaban Abba yakarasa sanan yazauna agefenshi yace "ina kwana Abba" sanan yakalli matar dake gefenshi yace "Ina kwana Mum" daidai lokacin dayan matar taja coffee table zuwa gaban mijin nasu ta dauramai tray akai tace "your food is ready Daddy Hamad" jaridan ya linke tareda mikamata, karba tayi dayan matan tadauke kai Abba kuma yatura hannu a aljihun sanan yaciro wasu kudi yamikama Hamad yace "inka kaisu kabiya musu kudin makaranta" sanan yajuya yakalli matar dake gefenshi yace "me yaran nan sukeyi asama har yanzu basusan zasu makaranta bane"? dasauri tace "kumafa su tuntuni sukai break, Nanaa, Hawwa" daga chan sama aka amsa, wasu yan mata manya masu jiki guda biyune suka sauko daga stairs, yaran zaka dauka yan biyu ne dan suna kama, irin kama na jini dinnan, Nana itace Babba 26yrs take tana final year a BUK tana karanta Mass Com, sai Hawwa 24yrs tana 300level tana karanta international relation itama a Ado Bayero, Hawwa na kama da Hamad sosai, dukansu suna sanyeda lemon green hijabi na haddan, dukansu ransu abace yake dan sun tsani zuwa hadda suna uni amman suna wani zuwa hadda shikuma Babansu yanuna babu wacce ta isa tabar hadda cikinsu kodako PHD sukeyi, tashi duka yaran sukayi sukama iyayensu bye suka fice, sanan Ya Hamad din yatashi yace "bari nakaisu Abba" gyadamai kai kawai yayi dan haka Babansu yake baifiye son magana ba, sanan yawuce yafice. Kaman ance tadaga kanta sama taga gittawan mutum dasauri an bude kofa anshige daki batare da an bari sun hada ido da Mami ba. Ahankali Mami tasauke ijiyan zuciya dudda bataga fuskanba but ko amafarki aka tadata tasan waye. Duk suna zaune afalon harya gamacin dumamen tuwon yadauki ruwa yasha, Dan gyaran murya matan dake zaune kusada shi tayi Mum tace "Alhaji nace bari namaka tuni, kaga duka duka bikin Nana bayan Babban salla da sati uku ne, gashi lokaci nata matsowa yanzu baifi wata daya bikin ba, nasan dama kariga kabada kudin kayan daki, cha kayi daman wanan satin zakaban kudin kayan kitchen, kaga idan kabani nida Zainab saimu shiga kasuwa yau muyo siyayyan koya kika gani Zainab"? Mum tama Mami dake zaune tana sauraransu magana, gyadamata kai tayi sanan tace "eh hakane Abban Hamad" ruwa yadauka a cup yakara kaiwa baki yasha sanan ya ijiye cup din, hannu yasa a aljihu yaciro bandir din yan dubu daya guda biyu yabata yace "kinemi wata kijeda ita kasuwa, Zainab bazata iya zuwa ba itakeda girki, kuma yau lahadi ina gida" yana fadin haka yatashi yawuce sama duk suka bishi da kallo, saida taga yashiga dakinshi sanan tabata rai tace "Alhaji Alhaji bantaba ganin kafaffen mutum irin shiba wlh" tashi tayi batare data kalli Mami ba tai stairs tabude bangaren ta tashige dan saman bangare biyune nata dana Zainab saikuma dakunan yaransu guda uku, na maza kanana dana mata kanana saikuma na yan matan suma dakinsu daban. Ahankali Mami ta tashi ta tattare duka kwanukan takai kitchen sanan tasa Mai aikinsu Uwani tazo tashare falon ta kunna turare sanan tai sama itama bude dakin mijin nata tayi tashiga bata wani dade aciki ba sanan tafito, direct dakin yan matan tayi ahankali tabude kofar, dakin nada dan fadi gashi a gyare Kal Kal, gadaje ne guda uku irin nayan boarding jere adakin kowanne da bangaren nashi saiga wardrobe na bango da kayan kowa keciki, bin kan gadajen tayi da kallo ganin babu kowa kai yasa takarasa shigowa dakin tareda maida kofan tarufo sanan tashigo ciki takaraso tsakiyan dakin saikuma ta tsaya turus tai shiru tana kallon gaban gadon dake tsakiyan dakin, wata faran budurwan yarinyace azaune akasa tabama dakin baya tana kallon bango tadaura kanta kan kafafuwanta ta, nimai rubutu M Shakur banmasan mutum bane awurin ba saida naga Mami ta tsaya turus tana kallon wajen, wani irin silk black gashin kaman na yar India ne zube awajen yana taba tiles din kasan daki sabida yanayin zaman datayi tsabagen tsayin gashin, sai farin kafanta sol mai bala'in kyau da dogayen fararen farcenta dababu komi akai sai uban haske kaman ana wankesu da madara. "Du'a" jin ankira sunanta yasa tadago kanta daga kifen dasuke akan kafafunta dasauri batare data waigoba jin muryan Mamin ta, dan Jim Mami tayi tana binta da kallo sanan asanyaye tace "inkin gama kukan ki tashi ki tattare gashin nan naki ki kulle kisa a hijabi kije Abban ki nakiranki yana dakin shi" tana maganan tawuce tafice daga dakin tarufo musu kofan. Ahankali takai fararen hannuwanta tashare fuskanta sanan tamike tsaye ahankali, wani iri mahaukacin cokacola shape Allah yamata gawani irin pointed curvy ass gareta daya fito sosai cikin doguwan rigan material din dake jikinta, itama kaman sauran yaran gidan tanada dan jiki danbazaka taba kiranta da mara kiba ba amman batakai su Nana kibaba, saidai tafisu diri, ga gashin kanta dabaida banbanci dana yan India har waist dinta, juyowa tayi ahankali TSARKI YA TABBATA GA ALLAH SUBHANAHU WATA'ALA WANDA YA HALLICI SAMAI DA KASSAI DAKUMA HALITTUN DAKE CIKINTA!!!! yarinyar nan koda ace itace tayi kanta banjin zatai kanta tai kyan datake dashi yanzu hakaba dan My Lord!!! dan itace definition of tacika goma cip cip tamakai sha uku, farace Kal fuskanta babu pimple ko daya idanunta sun kumbura sunyi ja sabida kukan datayi wanda haryau takasa sabawa dan by now yakamata ace tasaba duk sanda yan uwan ta zasu makaranta boko ko islamiyya saitai kuka, tanada wani irin long pointed hanci ga pink lips, gashin idanunta dogaye kuma acike sun jikeda ruwa, ga kirjinta awani irin cike kaman wacce taje tai surgery ga flat tummy kaman bata tabacin abinci ba, Allah yamata ass amman waist dinta kona jariri albarka her waist is so tiny, ahankali take tafiya har zuwa gaban madubin dakinsu ribbon dinta dake wajen tadauka sanan ta kulle kanta da kyar sanan tashiga bayinsu wanko fuskanta tayi tafito tadauki dogon hijabin ta maroon tasaka tafito daga dakin ahankali. Cikin wata irin siririyan cool melodious voice tai sallama gaban dakin Abban su, daga ciki taji yace "shigo" ahankali tabude kofa tashiga kanta akasa, yana zaune kan couch din dake dakin yabita da kallo tazo gabanshi tazauna tareda saukar da kanta kasa ahankali tace "Abba gani" zama ya gyara tareda bude Al Qur'ani dake kan cinyanshi sanan yace "biyomin haddanki" gyara zama tayi sanan tafara rairomai suratul Yusuf shafa'i ukun dayabiya mata last week, shi karan kanshi idan tana biyamai hadda baiso tadena dan muryanta Allah yay mata dadi saida tagama tsaf sanan yakara mata wasu shafa'i ukun kafin yamata tajweed sanan yace "tashi kitafi" tashi tayi ahankali tai hanyar kofa yasake binta da kallo harta daura hannunta kan handle din kofa taji yakirata anatse. "Du'a" dasauri tajuyoda kanta ta kalleshi saikuma tasauke idanunta kasa tace "na'am Abba" ahankali yace "nariga nasaman miki wata sabuwar malama, daga gobe zata fara zuwa In sha Allah, ki shirya" gyadamai kai tayi sanan tajuya zata bude kofan saikuma tajuyo ahankali batare data budeba ta kalleshi hada ido sukayi hakan yasa takasa magana tajuya zata bude kofan tafice cikin muryan nan nashi nabawasa yace "mekikeso ki fada"? Dan juyowa tayi ta kalleshi saikuma tasauke kanta kasa kirjinta na bugawa fat fat tashiga wasa da yatsunta tsabagen how nervous she was tama kasa magana, dan idan Abban su yakureka da ido zamaka iya fitsari ajiki baka saniba, shifa kokadan baida wasa kuma yanada zafi sosai, gashi kaifi daya saisa duka yaranshi ke tsoron shi. Ganin takasa magana yasa yace "I'm listening" rawa sosai muryanta yafara tanama bude baki maganan yakasa fitowa saikuma tasaki hannunta ta shiga chakuda hijabinta da hannu duk yana binta da kallo hijabin tarike gamgam sanan da kyar tasamu maganan yafito ahankali tace "Ab.....ba ni......maisa ake barina agida kahanani fita kowaje, Abba ni nafison naje school kaman su Ya Nana......" saikuma tasake hadiye wani irin dry miyau hawaye yawani zubo daga idanunta suka sauka akan hijabinta cikin wata irin murya na wacce ke gabda fashewa da kuka kuma take a bala'in tsorace tace "Ab....ba ni maisa baka sona kaman yanda kake son su Ya Nana da Hawwa da....d....." Du'a!! taji anwani irin kirata da kakkausar murya dayasa tadaga kanta da sauri ta kalli inda taji muryan, Mami ce tafito daga bedroom din Abba da alamu tuntuni take ciki maybe gyaramai dakin take dan taga karamin rag na goge goge a hannunta, cikin wani irin tsananin bacin rai tace "Du'a are you questioning your father? eh? mahaifin ki kika tasa agaba kina tuhuma haka?" girgixa mata kai tayi dasauri saikuma tasaki kuka dasauri tajuya tabude kofa tafita daga dakin dagudunta. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR UMMI COLLECTION is a whole world of turaruka, both na wuta dana feshi, exquisite burners na electric dana charcoal, and oils, turarukan wanka da sauran su. kunkosan kwanan nan UMMI COLLECTION na promo free delivery, hehehe banso kuyi missing this mad offer just click on this link danyin magana da ita directly. wa.me/+2348186968736 free page EPISODE 2️⃣ Azuciye Mami ta jefar da rag din dake hannunta tace "nikema yarinyar nan magana tafice tabarni sabida batada kunya Dadyn Hamad" tataho cikeda bacin rai zatai wajen kofa tabita Abba dake kallonta tunda tafara masifan yace "ina zaki"? Turus ta tsaya tana kallonshi takasa koda motsi, anatse yanuna mata bedroom dinshi yace "koma kicigaba da abinda kikeyi" dasauri tace "but......" "no buts ki koma kicigaba da abinda kikeyi nace" yay maganan babu alamun wasa akan fuskanshi hakan yasa bata karacewa komiba tawuce takoma ciki ranta abace, jaridanshi yabude ahankali yacigaba da karantawa bazaka gane takamaimen wani yanayi yake cikiba dan fuskanshi bata nunawa. Dakinsu tabude dagudu tashiga tafada kan gado tana kuka sosai, tayi kuka nakusan awa daya sanan bacci yay awon gabada ita akan gadon. Hayaniya yatadata daga baccin datakeyi, bude idanunta tayi ahankali saikuma ta yunkura ta tashi zaune tana kallon dakin nasu, Nana da Hawwa ne kecire kayan jikinsu sundawo daga hadda duk sunyi zufa, ahankali tace “Ya Nana kundawo daga makaranta” danjuyowa Nana tayi takalleta tana kokarin daukan zanin dazata daura tashiga wanka tace “eh yanzu muka shigo”"sannu da zuwa" tafadi ahankali sanan tajuyo da kanta Hawwa ta kalla taga Hawwa tadauke kai dasauri tana batarai, daidai lokacin aka bude kofan dakinsu, Aneela ce tashigo wacce take kanwarta, dan Du’a ce yar Mami tafarko, sai Aneela, sai Muhammad da Mudasir su Hudu Mami ta haifa, itakuma Mum itace mahaifiyar su Hammad, Nana, Hawwa, Amal, da Asiya yaranta biyar. Ko kadan Aneel bata kama da Du’a inba ma angayamaka ba bazaka zaci uwarsu dayaba dan tafi kamadasu Nana black beauty ce itama, kyakkyawan yarinya bakutu da ita, zama tayi kan gadon takalli yayartata tace “yauma saida kika kara kuka sabida muntafi makaranta banda keko” Hawwa data zauna kan gadonta tana ciro wayanta daga jaka tana kunnawa tace “asheko xakita kuka har karshen rayuwanki dan Abba yace konan da gate bazaki taba fitaba” turo baki Aneela tayi cikeda rashin kunya ta kalli yayartata saikuma takai hannunta tadaura kan kumatunta tace “karki kara kuka kinji Duudo, kinga ko yau Malam yafassara mana wata aya yace duk wanda yadogara ga Allah to hakika Allah ya isar masa, ki dogara ga Allah and I promise you Allah will be there for you, kiyita addu’a zakiga Abba zai chanza zaice kema kifara zuwa school kaman mu kinji” gyadama kanwar tata kai tayi ahankali, Aneela tawani washe baki tai murmushi hakan yasa itama tai murmushi, Subhanallah idan tai murmushi numfashinka zai iya tsayawa sabida kyan datake karayi. “In dauko mana abinci muci tare?” Aneela ta tambaye ta, Gyadamata kai tayi hakan yasa tasauka daga gadon tawuce tafita, itakuma ta sauka daga gadon ahankali sanan tawuce bathroom dinsu dan dauro alwala Hawwa tabita da harara wanda inda sabo tasaba tun suna yara basa shiri sabida sako da sako nesu dan daga Hawwa sai ita aka haifa agidan, itakuma Nana babu ruwanta bata shiga harkanta as per babban yaya in the house. Fitowa tayi ta shimfida dadduma tadau hijabi tasaka ta kabbarta salla daidai lokacin Aneela tashigo ajiye musu rice da stew din tayi akan gado itama tazauna tana jiranta ta idar, itakuma Hawwa ta tashi tafita duk ranta abace yake sabida yanda tadawo Mum dinsu batanan. Saida ta idar da sallan sanan tazauna sukaci abincin tareda Aneela batare dasunyi surutu ba sabida Nana dake waya da wanda zata aura, sosai taci abincin suka gama tass Aneela tafita da plate din takai kitchen sanan tasake dawowa dakin. Wuraren 4 Mum tadawo daga kasuwa da mota guda na kayan kitchen yaran sai murnan ganinta suke barinma yaranta dakin da ake tarin kayanta akakai komi bayan Abba yagani sanan daga ita har Mami suka shiga kitchen sukahau girke girke sabida bakin da Abba zaiyi yan wajen aikinshi da iyalansu, yaranma duk aka kirasu kitchen banda Du'a dakenan ita kadai adaki. Tana zaune adakinsu har magrib ita kadai, dan tun dazu aka kira Aneela da Nana da Hawwa duka batasan me akayiba but tadaiji kamshin girke girke kuma yawanci tasan ana irin girkunan nan ne idan zasuyi baki, tashi tayi ahankali ta shiga bayi wanka tayo tareda dauro alwala tafito daidai lokacin da Nana da Hawwa sun shigo dakin duksunyi zufa, dasauri tace “Ya Nana mekukeyi?” “Girki” tabata amsa atakaice tawuce tashiga bayi dan wanka itakuma Hawwa tazauna akan gado tana daukan wayanta tana dubawa ko ankirata, gaban wardrobe dinsu taje tabude bangaren kayanta, wani doguwan rigan atampa black taciro tawarware sanan tasaka dayamata kyau sosai sanan tadauki hijabi tajuyo hada ido tayida Hawwa dake kallonta suna hada ido tadauke kai tacigaba da danne dannen wayanta, saka hijabin tayi tahaukan dadduma tafara salla daidai lokacin Nana tafito daga bayin ta kalli Hawwa tace “tashi kije kiyi wanka Hawwa kinga Abba yace mu shirya dawuri suna hanya fa” tashi Hawwan tayi tashiga bayi itakuma Nana tashiga shiryawa cikin wata atampa. Idar da sallan tayi ta tashi tazauna akan gadonta tareda cire hijabin ta ijiye agefenta tana kallon yanda duk suke shiryawa agurguje, suna makeup abin na bata sha'awa dan ita mai kadai na shafawa gareta sai body spray, batada sauran kayan kwalliyan dasuke dashi kuma bata isa ta taba abinsu ba barinma masifaffiyan Hawwa nan. Daga Hawwan har Nana saka atampopi sukayi iri daya suka shirya tsaf gwanin ban sha'awa sanan kowacce ta zauna kan gado tana danna waya, sosai take kallon wayan dasuke dannawa, duk idan taga suna tabawa saita bata shaawa kaman taje ta karba amman tasan bazama su bataba, duk suna zaune ahaka kowa nawasa da wayanshi banda ita dake kallonsu kaman tasamu film aka bude kofa dasauri duk suka daga kansu suka kalli kofan, Abba ne yasaka lafiyayyan shadda mai ruwan toka da hula akanshi yana tsaye daga bakin kofa batare daya shigoba yakalli su Nana yace “kufito kugaida Abokan aikina da matansu” yana maganan yasaki kofan yay gaba duk tashi sukayi harda ita cikeda wani irin murna koba komi yau zataga wayanda bayan gidansu ba, hijabinta tadauka tasaka sanan tabi bayansu Nana dasukai gaba batareda sun cemata komiba suka fito Abba na tsaye kan stairs yana jiransu su fito yagansu, hada ido yayi da Du’a dake nonnoke kai, ahankali yace “ke banda ke koma daki ki zauna” wani irin murmushi Hawwa tayi ranta fess jin ankorata, Gyadama Abba kai tayi ahankali cikeda mugun sanyin jiki tajuya ahankali tashiga daki tareda maida kofan tarufo daidai lokacin Hamad yafito daga dakin Mum dinshi, hada ido Abba yayi dashi yace “let’s go tunda kafito” shida Abba suka jera yaran kuma abayanshi har zuwa kasa. Abokanen aikinshi ne su uku da matayensu da yaransu kanana suna ganinshi Babban cikinsu yace “what a nice family kakedashi HOD” dan murmushi Abba yayi yakaraso wajen yabasu hannu sukuma yaran suka shiga gaida kowa, Mami da Mum da Uwani suka shiga kawo abinci da kayan kwalama, ahankali Mami kebin kowa na falon da kallo saikuma tasauke ijiyan zuciya ahankali, daya daga cikinsu yace “wayan nanne kadai yaranka HOD”? Gyadamai kai yayi yace “eh” ahankali Mami dake kokarin bama matar abokinshi plate na snack tadan saci kallonshi saikuma tai murmushi tacigaba da serving while Abba yacigaba da magana yanuna Hamad yace “wanan shine first son dina Hamad he’s 30, yakaranta engineering” dasauri bakin sukace “like father like son” danshima engineering yayi yanzu shine HOD engineering department a BUK, murmushi yayi yace “yayi joining NDA yanzuma wani program yakeyi anan kano saisa yakenan, sai Aisha” yanuna Nana yace “muna kiranta da Nana dan tanada sunan Mamana, ankusa bikinta nan da bayan salla, sai Hawwa sai Du….” Shiru yayi dasauri saiya nuna Amal yace “sai Amal, Aneela, Asiya da Muhammad da Mudasir, yarana takwas” “wow masha Allah, nice family wlh, Allah ya rayamaka su kaga aurensu” murmushi Abba yayi yace “Bismillan ku mufaracin abinci” nan aka shiga cin abinci akai shiru, ahankali Hamad yatashi yay excusing kanshi yay sama binshi da kallo mahaifiyarshi tayi babu daman kiranshi sabida bakin dake wajen. Dakinsu Du’a yabude yashiga tareda maida kofan yarufe sanan yajuyo ya kalli gadonta, a kwance yaganta tarufa da hijabinta, ajiyan zuciya yasauke aboye sanan yashigo dakin yace “Hey Duudo look what i got for you” shiru tayi kaman tana bacci taki motsi, ahankali yasa hannunshi yakama kafafunta yadagasu sama sanan yazauna abakin gadon sanan yasaukar da kafafunta kasan gadon tareda saka hannu yaja hijabin data rufe fuskanta dashi, dasauri ta yunkura zata juya fuskanta kawai yadagota yace “come here Du’a” sata yayi ajikinshi kaman jira take ta kankameshi sosai sai kuka, ko kadan baiyi attempting hanata kukan ba, duk kanninshi babu wanda yakejin tausayinta yake kuma so kaman Du’a sabida tafi kowa rauni, he don’t care about kalaman da family su suke fadi akanta ana cewa itaba yar Abba bace, mayya ce, yar aljanu ce bla bla bla, all he knows is Mami da Abba suka haifeta and she’s his little sister kuma yanason kanwarshi sama da tunanin kowama. Cikin kuka tace “Ya Hamad ni wlh inaso namutu” dasauri yacirota daga jikinshi yace “ke are you crazy? Karki kara fadin haka” bayan hannunta takai tana share fuskanta tace “Abba bayasona, Mami bata sona, Mum ma batasona, Kaka ma batasona, kaga ni kadai Abba ya tsana ayaranshi, yakorani nakoma daki dazu, kuma kaga yace yaranshi 8 yacireni daga cikin yaranshi, kullum ina kulle adakin nan kaman mayya, dama Kaka tace ni mayya ce ni aljana ce, sabida ni kadai aka haifa daban bana kama daku does that means am a witch ko aljana eh Ya Hamad? Ya Hamad bakacemin kananan ranan da aka haifeni ba kuma kace Mami ta haifeni maisa su Aneela dasu Muhammad da Mudasir kadai takeso eh? Ya Hamad babu asibitin dake chanza kalan fatan mutum ka kaini naje nakoma kalan yan gidan mu sabida Mami na da Abba su soni nima eh Ya……..” hannunshi yadaura akan lips dinta yace “ya isa haka listen to me all abubuwan nan dakikaga Abba da Mami nayi bawaidan basa sonki bane sunayine to protect you, Du’a tun kina primary school ansha ayi attempting ayi raping naki nasan lokacin kina yarinya ba lallai kituna ba, but kin tuna lokacin dakike JSS 2 abinda teacher ki da Abba ya kulle yamiki ko” runtse idanunta tayi dakarfi alamun ta tuna, hakan yasa ahankali yakai hannunshi yakama hannuwanta guda biyu yace “listen to me, Abba is only trying to protect you, Abba bai tsaneki ba” ahankali cikeda raunin murya tace “amman yana kunyan ya nunani amatsayin Babana” tai maganan tana kallon Ya Hamad kurii da manyan idanuwanta dayasa yakasama mata karya dan to some extend all abinda take fadi gaskiyane, ahankali kawai yajawota jikinshi ya rungumeta yakai hannunshi yashafa gashinta murya chan kasa ta yanda dagashi sai ita sukeji yace “kin tuna abinda nake yawan fadamiki” gyadamai kai tayi ahankali ajikinshi hakan yasa yace “fada inji” murya chan kasa hawaye nabin kuncinta tace “Du’a kome kikaga yana faruwa arayuwanki Allah yasan dake, jarabawanki ne, karki kaucema Allah karki butulcemai, bake kikai kanki ba Allah ya yoki, love yourself, kiyi imani da Allah kikuma dage da addu’a watarana sai labari my beautiful little Duuudo” suka karashe maganan atare hakan yasa takara kankameshi, murmushi yayi sanan yacirota daga jikinshi, handkerchief yaciro daga aljihunshi yace “now let’s wipe those tears no more kuka okay” gyadamai kai tayi tareda murmushi yan kananun white teeth dinta suka bayyana, sharemata fuskan yayi tass sanan shima yamata murmushi yace “idan bakin nan suka tafi zan dauko miki sababbin novels din dana sayomiki kinji” gyadamai kai tasakeyi, kumatunta yaja yace “idan kika sake kuka saimun bata” dasauri tace “bazan sakeba” “kinci abincin dare?” Girgizamal kai tayi, tashi yayi yace “bari naje nakawo miki saiki bani labarin wayan nan novel din” gyadamai kai tayi yawuce yafita yana murmushi, Allah yamata brain, english novels yake sayomata dasukakai 1000+ pages cikin 2days tagama kuma tsaf zata bashi labarin novel din, abinda yataimaka mata da english ma kenan. Bai wani dadeba yadawo dakin da bowl na hadadden pepper soup da cow head, kafinma ya iso ta tashi tsaye dasauri tace “Ya Hanad kaman pepper soup ko” bata plate din yayi yace “mayyan nama kawai” dan tana balain son nama tun tana yarinya, murmushi tayi takarba dasauri tazauna tashiga ci ya tsaya shikuma yana kallonta, she looks so happy hakan made him so happy, dan yarinya ce da dawuya kaga she’s happy saisa anytime she looks happy happiness dinta is infectious sai kawai kaji kaima ka kamu da farin ciki. Juyowa tayi takallai tana tana naman kaman wata yar baby looking so adorable ganin ita yake kallo yasa tamikamai last piece na meat din tace “zakaci” hararanta yayi yace “marowaciya sai yanzu zaki bani to banci” dan dariya tayi tace “yakuri bari naci wanan gobe saimuci tare, Ya wai yaya ake dafa nama ne”? “Har yanzu ba’a barinki ki shiga kitchen?” Gyadamai kai tayi tace “ba Kaka tahana ba” gudun karta tunakomi dan yanzun nan kuma tahau kuka tasa yace “zan sayo nama saina koyamiki a kitchen din side dina” sosai tashiga jin dadi tana tauna namanta bude kofa akayi dasauri dukansu suka waiga, Mum ce fuskarta amurtuke, wani mugun kallo tama Hamad tace “mena gayamaka? Zokabar dakin nan” tai maganan tareda nunamai kofa, tashi yayi ahankali batare dayamata gaddama ba yazo yabita gefenta yafice, shigowa dakin tayi tazo har gaban gadon Du’a data sauke kanta kasa tana rikeda bowl din pepper soup din data cinye tace “ke bazakiji da bakin jinin ki kinemi yanda zakiyi ubanki yama yarda cewa ke yarshi ce ko yadinga lissafawa dake cikin yaranshi kina nan kina nema kisama dana bakin jininki ne, sabida kinga yanda ubanku keji dashi first son dinshi ga ilimi ga kyau shine zaki biyo tanan, to ta Allah batakiba bakar mayya kawai, kijechan kiji da kanki, na tsani uwarki amman naga matsalan da haihuwanki kesata ciki wlh har tausayamata nake, wayama sani ko wani aljaninne yadura mata cikinki dan naji ance tayi aljanu datana gida da kyar namijin dare yamabarta tai aure” ahankali tashare hawayen daya zubomata sharr babu abinda ta tsana irin adinga kiranta da yar aljanu ko mayu, Mum tasake wurgamata mugun kallo tace “wawiya dakikiya kawai babu abinda tasani sai zaman daki, kannenta ma sunfita iya karatu sunfiki iya komi Babanki yamaidake gidahuma yaryar aljanu kawai” wanan karan fashewa da kuka tayi sosai takai hannunta tadaura kan fuskanta tana kuka, murya chan kasa ta yanda Baza ajiba tace “niba yar aljanu bace” da sauri Mum dake tsaye kanta tace “me kikace Du’a? Mayarmin da magana kikayi? Did you just talk back at me eh?”. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR Don yin magana directly da M Shakur click on this link wa.me/+2347012181461 M Shakur nada group din Matan Aure wanda idan kinason kishiga is just 1k. hakama idan kinason advert shima M Shakur duk tanayi. free page EPISODE 3️⃣ Girgizamatakai tayi ahankali gwaninban tausayi alamun bada ita takeba, cikeda mugun tsana tace "haka zaki kare rayuwanki awanan dakin, agabanki yayyinki da kannenki duk zasuyi aure ke kina nan adakinnan har tsufa bazakiyi aureba saidai ko indaga dangin ubanki aljanune wasu zasuzo kuyi wup dake, mai bakin jini kawai mara kunya" tana maganan tawuce tafice daga dakin, sosai tafashe da kuka, har bakin suka tafi su Nana suka dawo dakin nan kuka take bata denaba, dayake sun saba bawai sabon abubane kukantaba saisaima babuma wanda yabita kanta saima shirin kwanciya dasuka shigayi suka gama Hawwa takashe wutan dakin, haka taci kukan nan har batasan sanda bacci yay awon gaba da itaba. Yau Monday sabida taci kuka batai bacci dawuri ba sai wuraren 8 ta farka, koda ta tashi babu kowa adakin saidai sababbin novels datagani manya guda uku agefenta dasauri ta tashi zaune ta dauka tana dubawa, sunan Novel din farkon The Noisy Naigbour, na biyun sunanshi the killer tree, saina ukun Disastrous Love, wani kalan murmushi tayi sanan ahankali tace "thank you Ya Hamad" ajiyesu tayi tawuce bayi alwala tadauro sanan tafito tai sallan asuba tabude Al Qur'ani tana koya Haddan da Abba yabata, saida ta tabbatar ta haddace shafi daya darabi sanan ta tashi, dakinsu ta shiga gyara musu wanda yanzu zata iyacewa a rayuwa that's the only thing data iya gyaran daki shima da karfi da yaji takoyama kanta, ta gyaramusu gado sanan tawuce bayi tayi brush tayo wanka tafito ta shafamai sanan tasaka wani riga da skirt na atampa daya mata kyau tai parking gashinta da kyar sanan tadauki novel kaman barauniya tabude kofan dakinsu ahankali sanan tasakai taleko kadan ganin babu kowa yasa tafito duka, sanan tashiga sadadawa tafara tafiya ahankali zatai stairs. "Ina zaki"? kaman daga sama taji muryan Mami dasauri tajuyo, hada ido sukai da Mami data fito daga dakinta tana kallonta, saukar da kanta kasa tayi tana kara kankame novel dinta ahankali tace "Mami good morning" batare data bata amsaba tace "wuce kikoma dakinku ga Uwani nan zansa takawomiki break" gyadama Mami kai tayi ahankali sanan tajuya zata koma dakinsu bintada kallo Mami tayi harta shige sanan tasauke ijiyan zuciya ahankali tawuce tasauka kasa, hada mata breakfast tayi kunun gyada da kosai, samin kanta tayi da daukan wani karamin plate tajuyemata ragowan naman da Abban su yarage sanan ta kwalama Uwani dake wanke wanke kira dasauri Uwanin tazo tray tabata tace "kaima Du'a abinci adakinsu" karba tayi tawuce sama bude kofa tayi tashiga tana kallon Du'a data bude novel tana karantawa, har gaban Du'a tazo sanan ta tsugunna ta ijiye tray din still kallon Du'a take, ahankali Du'a ta janye novel din datake karantawa daga kan fuskanta jin kaman ana kallonta hada ido sukayida Uwani, almost 2yrs Uwani na aiki a gidansu but she thinks yaune 3rd time datake ganin Uwanin hakan yasa cikin yar muryan nan nata tace "kece uhmm yama sunanki U....uuuuu...." takasa tuna sunan dasauri Uwani tawashe baki tace "Uwani sunana mai aikin gidan nan" gyadamata kai Du'a tayi sanan tasake maida fuskanta kan novel din tacigaba da karatun dan ko kadan batada surutu kusan cikin duka yaran tafi gado halin mahaifinta indai rashin surutu ne. Sosai Uwani takasa motsi daga wajen sai wani irin kallon Du'a take dabamatasan tanayiba, bude kofa Mami tayi ahankali ganin yanda Uwani ke kallon Du'a dabamatasan tanayiba dan ita karatun novel dinta take bilhakki yasa ta dakamata tsawa. "Uwani" firgigit ta farka daga dogon tunanin datake haka itama Du'a tadan firgita jin muryan Mami hakan yasa duk suka kallo Mami, cikeda bacin rai Mami tace "kin manta kinbar aiki a kitchen ne zoki wuce kifita" dasauri ta tashi ta taho tace "yakuri Hajiya" fita tayi Mami kuma ta watsa watsama Du'a data zubama mahaifiyar nata manyan fararen idanunta harara sanan tajuya tafice, tai kasa danso take tadaura girki, kitchen ta shiga tana duba naman data saka a wuta itakuma Uwani tacigaba da wanke wanke tana tunani sai chan tajuyo ta kalli Mami da hankalin ta kekan juya naman datake dake wuta tace "Hajiya" "ya akayi Uwani"? Mami tamata tambayan batare data kalletaba, tsayarda komi Uwani tayi tace "Hajiya kunada y'a haka maisa kuke boyeta wanan yarinya taki haka aiko shugaban kasa tafi karfinshi, maisa kuke kulle ta adaki haka" tunda tafara maganan Mami takasa cigaba da juya naman datake ta tsaya chak harta gama maganan datake sanan tace "ki tsaya a huruminki Uwani inba kinaso mu sallameki mu nemo watabane" dasauri tace "yakuri Hajiya tuba nake, kawai daman abin ya tsayamin araine" juyawa Mami tayi tacigaba da aikinta bata karabi takanta ba. ******************* Yau Friday Sunada wata al'ada agidan ranan jumma'a kowama gidan nacin gayun Jumma'a. Su Nana tun 11 suka dawo yau sabida lectures daya kawai sukeda shi, tun safe batai wanka ba sabida Novel din Disastrous Love datake karantawa daya daukemata hankali gabaki daya, su Nana ko harsun sake wanka sunci gayu abinsu sunfice daga dakin zuwa dakin Mum dinsu. Bude kofa akayi Mami tashigo daga bakin kofan ta tsaya binta tayida kallo sanan tace "yau bazakiyi wankan bane"? Dasauri ta ijiye novel din ta kalli Mamin ta dataci gayu cikin wata hadaddiyar bubu na shadda, tashi tayi dasauri tasauka daga kan gadon daga ita sai rigan baccin data saka iya guiwa, ahankali tasaukar da kanta kasa tana wasada yatsunta tace "yanzu zanyi Mami" tana maganan dasauri tajuya zuwa bathroom dinsu tabude kofa tashiga Mami tabita da kallo harzata bude kofa tafice saikuma ta dawo cikin dakin, gaban wardrobe din dakinsu taje budewa tayi ta tsaya tana kallon side din kayan Du'a, bangaren bras dinta ta kalla danta lura kwanan nan bata saka bra at all, daukan bra din tayi ta kalla sai lokacin tagane duk su mata kadanne saisa bata sawa kuma bazata iya fadan mataba, kwasosu tayi gabaki daya tadauki wani leda tazubasu aciki sanan tawuce tafita daga dakin, dakinta tashiga ta ijiyesu agefe sanan ta kwaso mata wasu new manyan bra masu kyau guda uku sanan tafito tadawo dakin, wardrobe din taje ta ijiye bra din sanan tazakulo mata wani lace mai bala'in kyau pink and white flowers dan tasan Du'a da hauka babu abinda ta iya kowani kalan kaya tasamu saka wa take, taciro tahada mata da sabon bra da pant tadauko ta ijiye mata kan gado, sanan tamaida wardrobe din tarufe takoma dakinta, kwalli tadauko mata sabo dawani sabon turare tadawo ta ijiye mata kan gadonta daidai lokacin tafito daga wankan daureda towel a kirji, juyowa Mami tayi takalleta daga sama har kasa, sunnar da kanta tayi kasa cikeda kunyan Mami tana gyara towel din dan bai rufe mata cinya da kyau ba kuma batasan zata sami Mami adakinba data maida rigan baccin ta, juyawa Mami tayi tafice abinta, dasauri tazo kan gadonta ta zauna, kwallin da Mami ta ijiye tafara dauka tace "laaaaa yama sunanshi irin nasu Ya Nana dasuke sawa a ido" wani irin murmushi tayi ta ijiye tadau kwalin turaren tana budewa tace "laaaa nima inada turare yanzu sunanshi Zara" budewa tayi ta ijiye cikeda farin ciki, agurguje tashare jikinta sanan tashiga shafa mai sabon bra tadauka tasaka aiko yamata cip cip lace din tasaka yamugun mugun mata kyau turaren ta tadauka ta feffesa yafi feshe goma sai murmushi take sanan tadau dan kwalinta da kwallin ta tafi gaban madubi, zama tayi tadauki comb taje gashin tayi sanan tai parking gashin da kyar sanan tadau dan kwalin duk yanda taso tadaura takasa daga karshe daurin yan kauye kawai tayi dan bata iyaba amman dudda haka tai kyau sanan ta bude kwallin taciro zata saka takai idanunta looking so excited kafin tasaka tawani tsirama idanunta ihu tayi sosai tawani zarooo hakan yasa tama tundaga idanun har zuwa gefen idanun har kunnenta bakin zanen layi, sosai ta kankame idanunta tana ihu ga radadi sai kuka batasan lokacin data mikeba tana tangadi tana ihu. "wayyo idanuna wayyo idonta" Mami da haurowanta sama kenan taji ihun ta dasauri tai hanyar dakin bude kofa tayi daidai yana shirin kuma kanta da bango tana ihu dawani irin sauri Mami ta tarota tana kokarin tallabo fuskanta tace "maiya sami idon"? Rirrike Mamin tayi cikin kuka tace "Mami idona zafi kwallin nanne ya tsiremin kwayan idanun" Mami na rikeda ita ajikinta tai bathroom dinsu da ita bude tap tayi ta tare hannunta ta debo ruwa wanke mata fuskan tayi tass sanan takashe tap din tana rikeda fuskan nata tace "bude idanun naga" ahankali tabude idanun kadan, aiko idon yayi jajir, kallon Mami tayi tanadan kyafkyafta idon tace "yadena zafi Mami" Mami na rikeda ita tafito da ita daga bayin zuwa gaban madubi zaunarda ita tayi sanan tadauki wipes din Nana data gani awajen tabude taciro kwara daya sanan takama fuskanta tagoge kwallin dayamata layi har kunnenta tagoge tass, sanan ta gyara kwallin dabama tasa a ido ba saidai kasan idanun sanan tadauki kwallin, habanta takama tace "bude idanun nagani" budewa tayi sanan Mami ta zizara mata kwallin aduka idanun rirrike Mamin tayi tawani tura fuskanta kan cikin Mami tace "Mami idona wani iri daman haka yakeyi wayyooo" chak Mami ta tsaya tamanta the last time da hannunta yama taba jikin yarta saiyau, firgigit kaman wacce ta tuna wani abu sai kawai ta hankadeta daga jikinta batare data kalleta ba tace "dau dankwalinki ki daura" tawuce tafita daga dakin, bin Mamin tayi da kallo sanan tajuya ta kalli Madubi kwallin sunma idanunta wani irin hadadden kyau, murmushi tayi tadauki dankwalin tasake mai wanan local daurin yan kauyen nan sanan ta tashi hijabi tasaka tai sallan azahar ganin biyu tamayi sanan ta tashi tacire hijabi taje tagaban window dakinsu ta yaye kannenta tagani su Aneela da Amal a compound suna guje guje suna wasa duk sunci gayu suma, hakanan taji inama itace komawa tayi tazauna sanan tadauki novel dinta tabude zata fara karantawa saikuma kannenta datagani a compound suka kara fadomata arai jitayi she's damn tempted to go out, maida novel din tayi tarufe sanan tamike tsaye tana rikeda novel din tabude kofa taleko ganin babu kowa yasa da sauri tafito ta maida kofan ahankali ta rufe sanan tai stairs dagudunta har tana neman faduwa tasauka kasa nanma babu kowa, motsi dataji daga sama anbude kofa taji muryan Mum tanama Nana magana "kinduba zobon dayasa kimai hope yay sanyi"? wani irin kwasa tayi dagudu tashiga kitchen dinsu gabanta nafaduwa, gani tayi anama girki a kitchen din ga hadaddun kula na baki dataga an jera asaman kan fridge tana mamaki baki zasuyi yaune kuma, jin muryan su sun sauko kasa yasa da sauri tabude kofan kitchen dazai sadata da backyard tafita dasauri tamaida kofan tarufo dasauri daidai sun shigo kitchen din sanan tawani irin kwasa da gudu taidan mini garden din da Abban su yamusu awajen yawanci weekend Abba nazuwa garden din yazauna yasha iska, is very small a portable ga flowers sosai na daidai kudi ba irin na masu kudiba, ko kadan bata lurada mutumba sabida tana gudu tana waigan bayane jitayi kawai tai tuntube da mutum taiwani irin tumble tasaman kanshi tatsallako gabanshi zatai baya ta fadi yawani irin rikota gam gam hakan yasa dankwalin kanta yawani irin zamiye yafadi kasa, novel din datake rikeda shi yawani fadi shima, yanda gabanta ke faduwa dan tariga tasarai fadi zatayi yasa ta kankame idanunta gamgam cikeda tsoro tana wani irin nishi da bakinta dake fitowa afili. Chak ya tsaya batare daya saki hannunta ba yake kallonta tundaga kan tattausan hannunta daya rike zuwa kyakkyawan fuskanta da yanda ta runtse idanunta cikeda tsoro tana nishi zuwa yanda jelan gashinta ke gogan kasan wajen. cikin wani irin murya yace "who are you beautiful lady"? jin muryan mutum wanda batasaniba dan duk azatonta da Abba taci karo danshi ke zama awurin nan danhar tasadakar yautamutu a hannunshi yasa tabude idanunta dasauridasauri sanan tawaresu sosai ta kalleshi hada ido tayi dawani kyakkyawan Matashi wanda akalla zaiyi mate din Ya Hamad dinsu yana sanye cikin wani farin yadi mai laushi sai zuba uban kamshi yake, kara zaro idanu tayi tana kallonshi batare datayi maganaba, murya chan kasa yace "who are you? what's your name Pretty Lady" kokarin fizge hannunta daga nashi tashigayi sanan tace "My name is Du'a" wani irin lumshe ido yayi yabude yana karabinta dawani irin mayen kallo yace "you have a very very, verrryyy beautiful name, keyar gidan nanne ko bakuwace ke" kokarin fizge hannunta take takasa sabida yanda yariketa gam gam tace "ni yar gidan nanne, nika sakenmini hannu intafi" ganin hankalin ta nakan hannunta dayaki saki yasa yace "kinaso in sakenmiki hannu"? gyadamai kai tayi batare data kalleshiba ta kalli gefe daya, yace "to answer my questions saina saken miki hannu" dasauri ta gyadamai kai tana kallon gefe dan batason hada ido dashi sabida kallon dataga yanamata ahankali yana kallonta still yace "ke kanwar su Hamad ne"? dasauri ta gyadamai kai alamun eh hakan yasa yace "amman your mum is different ko?" sake gyadamaikai tayi tace "Mami ce Mum dina" yanda take magana da muryanta kaman na yara tsabagen dadi bala'in tafiya dashi yake she talks kaman yar yarinya kuma kaman ashagwabe, ahankali yace "Yaya akayi to bansanki ba?" ahankali tace "Abba baya barina infita" yanda take maganan gabaki daya taki kallonshi sai gefe take kallo yasa yasake binta dakallo tundaga gashin kanta har zuwa kirjinta da yake hango tudun boobs dinta da kyau wowwww! dan he could have a clear sight saman sabida yanayin wuyan riganta dakuma yanda tadan rankwafo ta gabanshi, tana kallon gefe still tace "dan Allah kasakeni in tafi I don't know you, idan wajen Ya Hamad kazo kaje side dinshi Abba kadai ke zama anan" murmushi yamata ganin da gaske takasa kallonshi sai gefe taketa kallo tana magana this girl is not use to men! yay maganan aranshi sanan yace "ni wajenki nazo sonki nake" girgixa mai kai tayi dasauri tace "wlh bani bane banama fita baka sanni ba please kasakenmini hannu nakoma cikin gida ba'a san nafitoba wlh" yanda take maganan yake mugun burgeshi baisan lokacin dayace "antaba gayamiki u look beautiful whenever you talk? Is this ur natural hair"? yakai hannunshi zai taba kanta dasauri takoma baya saikuma tasaki kuka shima binta yayi tana komawa baya yana kokarin biyota zai taba mata gashin sukaji karan fadin abu dasauri dukansu suka waigo baya. Nana ce tafito taci uban gayu sai kamshi take zubawa tadauko hadadden tray da jug din cold zobo da cups kekai dukta sakesu akasa jug din yafashe zobon nabin kasa. 💫 MY BEAUTY MY CURSE 💫 ✍️M SHAKUR Free page EPISODE 4️⃣ Ganin Nana yasa takara karfin kukan tace "Ya Nana kinga wanan mutumin ko yarikeni yaki yasakeni tundazu" juyoda kanshi yayi yana kallon yanda take magana kaman zai cinyeta yace "inda nasan akwai kyakkyawan yarinya irinki agidan nan I wouldn't have wasted my expensive time on this your sister yanuna Nana" wani irin kwalalo idanu tayi sai yanzu tagane saurayin Nana ne wanda zata aura, rawa jikinta ya shigayi tana kallon Nana tana kokarin fizge hannunta daga nashi, ganin yanda ta daburce yasa yasaketa yana murmushi looking so damn happy, dawani irin gudu ta kwasa tama kasa komawa ta hanyar data biyo dazatazo kawai ta zagaya takoma ta compound tabude kofan falonsu ta shiga da gudu tai sama. Binta yayi da kallo harsaida yadena hangota sanan ahankali yakalli dankwalinta dake wurin da novel dinta yadauka sanan yakai dan kwalin kan fuskanshi yana wani shakan kamshinta sanan ya janyesu daga kan fuskanshi yakalli Nana dake tsaye takasa kwakkwaran motsi yace "so kinada this beautiful sister baki taba gayamin anything about her ba, in fact you've never mentioned her to me ma" tattaro courage dinta tayi tasakinmai murmushi kobakomi akwai one thing data koyo daga wajen Mum dinta is kirsa, karasowa tayi kusada shi tazauna akan carpet din data shimfidamai cikeda salo irin na siyasa tace "ko Abban mu dudda yarshi ce baya acknowledging nata cikin yaranshi, bama Abba ba har uwarta Mamin ta data haifeta ma, bakaganta ba kaman mayya, Mamanta kafin tai aure tanada aljanu namijin dare, kafin acire mata aljannun akwai wanda ya aure ta so ance shine yamata cikin wanan yarinyar saisa gatanan daban, gabaki dayan danginmu ita kadaice fara, ita kadaice daban, kamanninta komi nata daban, Kakanmu ta tsaneta, she has been nothing but a bad luck duk inda tashiga saitai causing trouble saisa Abba yay grounding nata, ba boko ba islamiyya ko this our compound she's not allowed to come out, iya kanta daki, ko kitchen ba'a bari tashiga kartaje ta kashemu, I don't think ko hot water ma ta iya boiling, she has been grounded like this for years ba tun bayan JSS2" tunda take magananan yake kallonta don shi mugun dan gayu ne dan boko yaron dan gata dan masu kudi wani irin tabe baki yayi yace "you people are being sarcastic, young innocent preety girl zaku kulle haka agida sabida she's different kamanninta daban that's illiteracy, gatanan so pretty my lord, her body is so soft, ga gashi, just look at her snatch waist, ka auri wanan ai zaka more rayuwa da itane kasha miya kasha miya harka gaji" murmushin yake tayi tace "common Muhsin mubar maganan yar Aljanun nan" mikewa tsaye yayi yace "I'm being serious ni, wai kinzaci wasanake, wlh naganta inaso nafasa aurenki, bari naje nasanar da Dad, this ur beautiful sister nakeso wlh ita zan aura, gata so young daga gani batafi 20 ba" tashi tayi dasauri kirjinta na bugawa uku uku dan arayuwanta tana bala'in mahaukacin son Muhsin kaman zata haukace, yarone ga kudi ga gata ga kyau, dawani irin sauri takama hannunshi tarike tace "please Muhsin inma wasa kakemin this joke is way too expensive, bikinmu duka duka baifi 1month bafa saikace kafasa aurena kanwata kakeso daga ganinta yanzun nan don't you see what's going on abinda yasa ake cewa ita yar aljanune, minti nawa da ganinta har kaji kana sonta u are willing to risk our relationship damuka raina for years when we are finally about to get married, dan Allah karkamin haka, kataimakama rayuwana Muhsin kasan yanda nake sonka please Baby" fizge hannunshi yayi yace "stop talking nonsense, wlh bazan aureki ba kinjima na rantse, ni Du'a nakeso ita zan aura" yajuya zai tafi dawani irin sauri tasha gabanshi ta zube ta hanyar kneeling down tahade hannayenta tana kuka tace "please stop saying kanwata zaka aura, please stop saying that, wlh karabu dani zan iya mutuwa Allah kuwa Muhsin dan Allah karkamin haka, you know how much u mean to me eh, me zakayi da ita? babu abinda banfitaba kawai saidai ta nunamin haske" zaro ido yayi yace "what! are you crazy, karki kara comparing kanki da yarinyar nan dan wlh tafiki komi, nima daman zan aureki ne because u are full dan banson mace ramamma, kinada big boobs da ass you know that's what I like, but damn!!!! Du'a shape is bura'uba! her shape is life threatening, idan bansami yarinyar nan namore rayuwa da itaba I can die, ke kinga ass da boobs wane naki, see maddd flat tummy, see snatched waist, I don't think kugunta yakai 10, ke abeg go gefe we are talking about Kim Kardashian anan danko Kim taga Du'a she go run go hide" dasauri tashiga hade hannayenta zatai magana hankadeta yayi yabita gefenta yawuce yace "saikuma kiyi bayan nagama rantsuwa cewa bazan aureki ba kome zakiyi saidai kuma kiyi ni kanwarki nakeso wlh, am off zanturo Dad anjima da night" yana maganan yay gaba zuwa compound dinsu yaje yashige hadaddiyar jeep dinshi mai gadi yabudemai gate yawuce yafita abinshi. Takai morethan 15min awajen kuka take sanan wani irin zuciya yadibeta ta tashi tai ciki ta kofan kitchen tabi Mami na kitchen tana kwashe abinci amman ko kallonsu batayiba tana kuka tawuce fuuu ta tafi falo tashiga Mum dake zaune tareda Hawwa suna magana ne sukaga shigowan Nana tana kuka sosai bamata luradasuba tai hanyar stairs dasauri Mum tamike tace "Nana ke lafiya gani nan anan, menene kike kuka haka"? dawani irin sauri tajuyo tadawo batai wata wataba tafada jikin Mum tazube sai kuka, daga Mum har Hawwa rudewa sukayi, Hawwa tace "Ya Nana menene fada kukayi da Muhsin ne" cikin kuka sosai tace "Mum Muhsin yace yafasa aurena wai Du'a zai aura" chak Mami datafito rikeda kula ta ijiye kan dinning ta tsaya dubus awajen tana mamakin mekuma yakawo sunan Du'a a zancen su. Mum dama tarude sabida yanda yarinyar ke kuka tace "Du'a kuma, ta ina Muhsin yasan wata Du'a dahar zaice miki zai aureta iyye, kinsan mekike fadi kuwa"? Mum tai tambayan sounding so confuse and shocked dan batagane kan zancen yartataba, cikin kuka sosai Nana tace "Mum bayan nadauki zobo naje kaimai ajikinshi naga Du'a suna hira haryanama tabamata gashi taciremai dankwali, kuma idan karya nayi kije garden tama barmai dankwalin ta har novel dinta awajen ma" cikin wani irin mugun zuciya jikin Mum har kyarma yake tashiga kwalama Du'a kira. "Du'a! Du'a!!! ki sauko kasan nan dakanki kafin nazo dakin nan wlh dan na lahira zai fiki jin dadi" bude kofa tayi ahankali tashiga saukowa idanunta sunyija sabida kuka tashiga saukowa daga stairs hada ido tayida Mami dake tsaye a dinning tana kallonta kaman yanda itama take kallon Mami, kasa karasa saukowa tayi Mum tace "zaman lafiyanki shine ki amsa tambayan dazan miki batare dakinmin karyaba inba hakaba yau saina kusan nakasaki wlh, kin sauka kasa ko baki sauka kasaba"? kama jikin skirt din lace dinta tayi gam gam tsabagen tsoro tana kallon Mami tsabagen tsoro sanan ta kalli Mum tace "bayan nai salla shine ta window na leka naga su Aneela nawasa a compound shine nasaci hanya ta kitchen nafita, to naji muryanku a kitchen shine na kwasa da gudu sabida kada ku ganni wlh wlh ni bansan da mutum a garden ba tuntube nayi dashi zan fadi shine yataroni" fashewa da kuka tasakeyi sosai tace "wlh wlh ni banma sanshi ba Allah kuwan Mum" Cikin wani irin bakin zuciya Nana tai inda take a stairs wani irin finciko gaban riganta tayi ta chakumeta tace "karya kike baki sanshi ba, kinji ina waya dashi jiya da daddare munyi zaizo yau saisa yau harda cin kwalliya haka sabida ki kwacemin wanda zan aura ko, baki sanshi ba ubanme mikikeyi ajikinshi"? Cikin kuka sosai tace "wlh Ya Nana niban shiga jikinshi ba hannuna yarike kuma inata kokarin na kwace yaki sakina, shine yazo zai tabamin gash......" wani irin kishine ya kwashi Nana tawani kaimata mugun duka abaki bata cire hannu ba sai jini bakinta tasake fashewa da kuka, kimarta Nana tashiga yi baji bagani Mum tace "yima shegiyar yar Aljanun mugun duka Nana, yimata jina jina, itada uwarta sunga kinyi miji daga gidan arziki shine aka turata tayomiki kwace tarabaki dashi, duniya inhar baka mutuba baka gama ganin abin kallo ba, kimeta da kyau kyan datake takama dashi ki chanza mata halitta" yanda Nana ke dukanta tana bubbugata da kome tasamu yasa tafara ihu tana mika hannu tana kwalama Mami kira dan bata iya fadaba bamatasan yanda zata fara dukan yartaba kwata kwata, ahankali Mami tajuya tacigaba da arranging dinning table din datake, kannensu dake wasa ihun dasukaji yasa duk suka shigo ciki suka cika falon, Aneela tafashe da kuka sosai ganin yanda ake dukan yayarta. Juyawa Mum tayi takalli dining ganin Mami tajuya tacigaba da arranging dinning abinta yasa tai wani irin murmushin mugunta tace "barka mata shegen rigan nan dataje tana kokarin kwacemiki miji dashi kannenta suganta taji kunyan duniya" wani irin bugata da tiles Nana tayi jikake kum Nana tawani juyarda ita tawani yage zip din riganta tanajan rigan zata ciremata, rike rigantayi tana kuka sosai tace "Ya Nana yakuri, Mamiii" tasake kwalama Mami kira dan mugun kunya take aganta, Mum da ranta fess dan tadade tanason gumama Mami amman tarasa ta yanda zatayi saiyau Allah yabata dalili mai kyau tace "fizge rigan duniya da kannenta suga abinda take boyewa, haka akema yan iskan yara masu son kacema yayyinsu mazajen dazasu aura, fizge rigan kannenta suga nonuwan marasa fasali" fizge rigan Nana tayi tayar Mum tace "yara ku kalleta kumata woyiiii" su Muhammad sukahau woyiiii dan basusan meke faruwaba yarane, throw pillow kan kujera taja takankame tana boye kirjinta, Nana tawani sake dauketa da mari tahau ruwan cikinta tana nausa daidai lokacin Abba da Hamad suka shigo dakin, shiru yaran dake woyi sukayi jikake dakin kaman andauke wuta sai muryan Du'a da baima fitowa da kyau tana kiran Mami Mami take, awani irin zuciye Abba yay wajen wani irin dago Nana yayi tsaye sanan yakai mata lafiyayyen mari Pau!!!!!! Dasauri Mum tace "idan duka zakayi Alhaji ni zaka daka danni nasa Nana tama shegiyan makiran yarinyar nan duka tacire mata riga kannenta sumata ihu" wani irin kallon Mum yake kafin yabi kowana dakin one by one da kallo sanan idanunshi suka sauka kan Mami dake dining tana arranging kula cikin kakkausan murya yace "Zainab kina nan wajen kina tsaye zasu kashe Du'a can't you intervene, wani irin banzan hali ne wanan" juyowa tayi takalli Abba idanunta sunyi ja sosai cike da tsananin kunci tace "Dadyn Hamad mekakeso nayi eh? mekakeso nayi? Ya zanyi da raina?Tun ranan dana tsugunna na haifo wanan yarinyar duniya nake shiga bala'i kala kala? Babu kalan shairin da ba'a yimin ba kan haifo yarinyar nan, tunda na haifi Du'a ban kara samin kwanciyan hankali ba, kome yasameta ita tajama kanta kahanata fita waje ubanme yakaita garden? Gasu gatanan idan suka kasheta kaga kowama yahuta daman tun ranan dana haifota tazamema kowa kashi a wuya ankasa taunata, ankasa fitoda ita, ankasa hadiyeta, nima nagaji I am tired of everything, I'm tired" kawai saiga kuka yazo mata dasauri tabar dinning din tawuce sama tabude dakinta tashiga abinta. Juyoda kanshi Abba yayi yakalli Mum da Nana dake kuka itama yace "kuwuce kuje kujirani adakina" wucewa sukayi sama, sanan ya kalli yaran yawani daka musu tsawa yace "to your room dukan ku" dasauri kowa na falon ya watse, Abba yajuyo yakalli Hamad yanunamai riganta yace "bani riganta" wucewa yayi yadauko rigan shikuma Abba ya tsugunna yatallabota zuwa jikinshi yana kallon fuskanta yanda goshinta ya kumbura ga bakinta jini, gefen fuskanta yay ja sosai, bashi rigan Hamad yayi Abba ya karba sanan yakama hannunta yasamata rigan kafin yarufe mata kirjinta dashi sanan yaja throw pillow data rufe kanta dashi ya yar sanan yasamata dayan hannun rigan yadagota zai saka mata zip tafashe dawani wahalallen kuka sosai ahankali Abba yace "ina ke miki ciwo"? Cikinta ta nunamai, daga riganta yayi yakalli cikin ga alamun naushi nan duk sunyi jajja, Hamad dake tsaye kansu yace "Abba bazamu kaita hospital ba kuwa what if tanada internal bleeding" girgiza mai kai Abba yayi yace "get me a towel and hot water da rob" wucewan kitchen yayi dasauri yakawo ruwan zafi da towel. Karba towel din Abba yayi sanan yasa a ruwan zafi yaciro yadaura kan cikinta yana matsamata fashewa da mugun kuka tayi tarike Abba tace "wayyo Abba zafi, Abbbaaaa" sosai ran Abba yabaci kuma yay alkawari saiya mugun sabamata, tun tana kuka yana fitowa harya dena saidai hawaye, saida yagasa harda goshinta da bakinta sanan yashafa mata rub din tass, sanan yakalli Hamad yace "kaje phamarcy and get drugs for her she can't go to hospital" gyadamaikai Hamad yayi sanan yawuce yafita shikuma Abba yatashi daukanta yayi tana jikinshi dantamayi bacci kwantar da ita yayi kan gadonta sanan yasa bargo ya lullubeta yadade tsaye akanta sanan yawuce yafita daga dakin. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR Free page EPISODE 5️⃣ Dakinshi yawuce, bude kofa yayi yashiga dakin Mum na zaune kan kujera itakuma Nana tana zaune akasa tana share hawaye danhar lokacin kuka take ganin Abba yashigo yasa gabanta yacigaba da faduwa dan gabaki dayansu suna tsoron mahaifinsu danko kadan baida wasa sanan yanada zafi. Maida kofan yayi yarufe sanan yashigo ciki har lokacin kanta nakasa sanan yawuce yazauna kan kujeranshi yana facing bata, cikin kakkausan murya yace "maiya hadaki da kanwarki Du'a Nana"?Hawayenta tashare cikin sheshekan kuka tace "Abba dazu Muhsin yazo na shimfida mai dadduma a garden shine nakoma nadauko zobo ina zuwa naganshi tareda Du'a....." yanketa Mum tayi tace "fadama Babanku komi kina bobboyemai kikaga dai Du'a ajikinshi" wani irin kallo yama Mum sanan yace "kika kara magana batare danabaki izinin kiyiba wlh saikinyi mamakin abinda zan miki" yajuya yakalli Nana yace "ina jinki" sake share hawaye tayi tace "Abba tarena ganshi da Du'a babuma dan kwali akanta yarikemata hannu yana kokarin tabamata gashi, shine Du'a na ganina tahau kuka wainace yasaken mata hannu, sakinta yayi ta tafi shine yacemin waishi bazai aureni ba wai Du'a yakeso ita zai aura yanzu bayasona waizaije yagayama babanshi" shiru tayi takai bayan hannunta ta goge wasu sababbin hawayen dasuka zubomata. Gyara zama Abba yayi ranshi amugun bace yana kallonta yace "dago fuskanki ki kalleni nan" girgixa mai kai tayi takasa, hakan yasa yadaka mata tsawa yace "I said look at me" dasauri tadago kanta takalleshi jikinta har bari yake tsabagen tsoro da shakkan Abban ta yace "so sabida namiji ne kike neman kashe blood sister ki, da Allah bai kawoni gidan nanba dayau kinyi kisan kai eh!" yasake dakamata tsawa kana ganin yanda yake maganan kasan ranshi abace yake, yace "to the extend kina ciremata riga exposing your fellow sister body kannenku su ganta, Nana is that how I train you eh answer me" fashewa tayi da kuka sosai tace "Abba kayakuri bazan karaba" girgixa mata kai yayi yace "kece y'ata mace tafarko yau idan namutu I believe kece zaki kula dasauran kannenki u will be their mother but look at what you did today, sabida namiji eh? sabida yace bazai aureki ba and so what zaki kashe yar uwarki ur blood sabida wani eh? Saina hukuntaki sosai Nana, stand up jeki kawomin wayanki, your laptop ki kawomin ATM card dina danabaki" fashewa tayi dakuka sosai dan babu abinda yafi tadamata da hankali irin wayan dawani wayazata kira Muhsin su shirya, ita karan kanta Mum saida ta girgixa amman takasa magana dan taga ranshi inyay dubu yabaci. cikin kuka Nana tace "Abba dan Allah kayakuri nayi kuskure amman namaka alkawari bazan karaba" wani kallo yamata yace "you know my principle bana dukan yara, but kika bari natashi daga wajen nan batare dakinje kin kawo what I asked for ba sainamiki jina jina" wani kallo Mum tamata na alamun taje takawo hakan yasata tashi tafita bata bata lokaci ba tadawo takawo komai kujera yanuna mata yace "keep them there and leave this room, sanan dagayau!" yajuya yakalli Mum yace"ki sallami Uwani duk wani aikin Uwani ita zata dingayi bazatabar gidan nanba saita gama kodako zatai lattin lectures get out" dasauri tajuya tafita tarufo musu kofan. Wani kallo yabi Mum dashi yace "I am so disappointed in you Hajara, halinki nabani mamaki and ki sauraren kiji bazan zauna inaji ina gani ki rabamin kan yarana ba, wlh duk randa kika kara attempting abinda kikayi yau kinasa anacirema yarana mata kaya kina kiran yara suyi ihu wlh wlh saina rabu dake take this as a warning" cikin kwantar da murya tace "kayakuri Alhaji na yarda nasan nai kuskure I know I took everything far, but raina abace ne maganan da Kaka keyawan fadi duk yadawomin kai, wlh Alhaji da gaske Du'a yar aljanu ce to inba hakaba ya za'ayi Muhsin dake tareda Nana kusan sjekaru biyu kenan yau kawai daga ganin Du'a yace ita yakeso yafasa auren wacce yasani for years, dududu bikinsu saura wata daya, tuntuni Kaka tace ka tattara yarinyar nan ke korata chan duniya inba hakaba bala'i da masifu iri iri sundinga samunta gidan nan kenan, yanzu maganan Muhsin baiwani dadani da kasaba amman what if dagaske yake eh? da gasken gaske yake shi yafasa auren Nana Du'a yakeso bahakan ya tabbatar mana itadin yar Aljanu bace ba kenan, wlh indai aka fasa auren nan saina kira Kaka na sanar da ita komi gwara tun yanzu nagaya maka sabida kar bayan kaji nayi kaga kaman na yaudareka ne" "tashi kifita daga dakin nan" Abba yay maganan cikeda fada, tashi tayi tace "narasa me kakeyi da yarinyar dakai karan kanka kasan bataka bace agidan nanba saisama baka ambato sunanta cikin y'ayan ka, hakanan wlh koma mezai faru saidai yafaru I am a mother bazan zauna inada zankada zankadanyanmata ba sukasa aure ba sabida yar aljanun da aka haifa maka agidan nan, gaskiya nake fadi I can go to any limit dannai protecting yarana, grounding nata adaki doesn't solve anything dan gashinan fita take causing trouble, the best thing is tabar family mu takoma chan family su na aljanu" tai maganan tana bude kofa tafice abinta, gabaki daya duka abinda tafadi yajisu. Ajiyan zuciya yasauke ahankali tareda fuzarda iska daga bakinshi yadade ahaka zaune sanan yatashi kaman an tsikareshi, bude kofa yayi yafice, hanyar dakin Mami yayi, ahankali yasa hannu yabude dakinta wani kamshi ne yamai sallama, shiga ciki yayi tareda maida kofan yarufe, tashi tayi tsaye daga kan gadon datake zaune idanunta sunyi jajir takakalo murmushi tace "sorry Dadyn Hamad bankawo maka abincinka ba" tazo da sauri zatabi ta gefenshi tawuce hannunta yakamo sanan yajawota jikinshi fuskanta ya tallabe yace "you've been crying ko jibi yanda idanunki suka kukkumbura" girgizamai kai tayi zatai magana saiga wani kukan kuma hakan yasa dasauri yasata ajikinshi yana bubbuga bayanta batare dayayi magana ba, tadade ahaka sanan tadago ta kalleshi tace "Abban Hamad kafin muyi aure ai kokai saida aka tabbatar maka dana warke ko naji sauki, babu any form of jinn ajikina, bana wasa da azkar safe rana da dare, yau shekara nawa muna tare ba kara having any form of attack ko mafarki ba, but yau nafara tunanin kodai sune baban Du'a di......." hannu yadaura mata akan baki yace "shiiiiii banson maganan nan, kintaba ganin jinn sun haifi mutum? nine mahaifin Du'a, kawai Allah yabamu y'ace daban damu nothing more nothing less" girgizamai kai tayi tace "what if Muhsin da gasken yafasa auren Nana Yaya zamuyi? how are we going to explain this to the family Yaya zamuyi" saiga wasu sababbin hawayen, yatsanshi yakai yasharemata hawayen daya zubomata yace "when we get to the bridge we will know ta yanda zamu tsallaka shi karki damu kanki kinji" gyadamaikai tayi ahankali wasu hawayen na zubo mata tace "Dadyn Hamad Du'a batajin magana, we've grounded her for years now tundaga JSS3 har zuwa yau, amman kwanan nan tasoma sneaking tana fitowa, hakanan inaji araina something is about to happen, what if tasake samin attem........." hannunshi yadaura kan lips dinta yace "stop talking, and stop thinking negative, idan tafarka nida ita we will have some serious talk, yanzu all abinda nake bukata is natsuwa dan banda ita ko kadan, ina bukatan natsuwa sanan nasamu nayi tunani, bari nasami natsuwa dake" yana maganan yadauketa zuwa gado bashi yafito daga dakinba sai wuraren 5 ya chanza kaya zuwa jallabiya fuskanshi tayi wani annuri alamun akwai full natsuwa taredashi yasauka zuwa falo, Mum na zaune a falo tadauke kai kaman bata ganshi ba. Saukowa Mami tayi taci sabon kwalliya Mum tabita da harara tace "kidaiyi kigama gobe zan karbi girkin" serving Abba tayi sanan tazauna gefenshi tana bashi duk wani abu dayake bukata. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR Free page EPISODE 6️⃣ Bayan sallan isha'i Abba baima dade da dawowa daga masallaci ba shida Hamad dasu Muhammad ba mai gadi yayi sallama izini Hamad yabashi yashigo, shigowa yayi har gaban Abba yace "barka da hutawa Alhaji, kanada baki, sunce wai Alhaji Ibrahim mai tabarau ne" kallon Abba Hamad yayi yace "Baban su Muhsin ne Abba" tashi Mum dake zaune afalon tayi ta kalli su Muhammad tace "yara kuwuce mutafi sama Abban ku yay baki" binta yaran sukayi sukai sama, kallon mai gadi Abba yayi yace "kamusu iso" Maigadi yawuce yatafi, Hamad yakalli Abba dayaganshi anatse yace "Abba yaya zamuyi idan dagaske Muhsin yake"? Murmushi Abba yayi bai bashi amsaba yace "just stay here and learn, duk randa bani kaine zakai making decision akan kannenka mata" gyadama Abba kai yayi daidai lokacin mai gadi yay sallama yabude kofa yashigo dasu hakan yasa Abba da Hamad suka tashi don agaisa, wasu Manya manyan attajirai ne su uku sai Muhsin dake taredasu kana ganinsu you don't even need an explanation kasan masu hannu da shuni ne, hannu Abba yamika musu cikeda girmamawa suka gaida dan mahaifin Muhsin ne Alhaji Ibrahim maitabarau sai kannenshi guda biyu Alhaji Isyaka Maitabarau sai Alhaji Mubarak Maitabarau, sosai Abba yagaisa dasu cikin mutuntawa yasa suka zazzzauna Muhsin shima ya gaida Abba cikeda girmamawa ya amsa, Hamad ma yagaidasu suka zauna cikeda girmamawa, shigowa Uwani tayi takawo drinks da ruwa sanan tawuce falon yay shiru. Gyaran murya Mahaifin Muhsin yayi yace "To bari mufara da kalamai mafi kyawu wato da Sunan Allah Mai Rahama Maikuma Jinkai, Alhaji kaganmu agidanka da dare haka kuma unannounced ko, bawani yakawomu nan ba sai wanan yaron" yanuna Muhsin dake gefenshi da kanshi ke kasa, sanan yakara sauke ijiyan zuciya yace "wlh Alhaji idan nace namasan ta yanda zanmaka bayanin nan kafahimta tonamaka karya amman bari nafara da tantance gaskiyan lamarin kafin nakoro bayani" yay dan shiru kafin yanisa yakalli Abba kaman yanda shima yake kallonsu yace "Alhaji wai dan Allah kanada y'a mai sunan Du'a ne? Danni wayanda muka sani shine wanan Baban dan naka wato Hamad, Aisha, Hawwa, Amal, Aneela, Asiya da Muhammad da Mudasir, dan Allah katabbatar min da gaskiyan lamarin nan kanada y'a mai sunan Du'a ne wacce duk bamusanta ba"? Shiru Abba yayi yana kallonsu kaman bazaice komiba danhar dagakai Hamad yayi yana kallonshi sanan yadan nisa yace "eh inada y'a mai sunan Du'a" ahankali Baban Muhsin yace "to Alhamdulillah, nasan banida wanan hurumin dazan tambayeka maisa baka taba ambato mana itaba ko wani abuba dan nasan kanada dalilinka nayin hakan, daman tabbatarwan kawai ita nake bukata tunda yanzu ka tabbatarmana kanada y'a mai sunan Du'a toga dalilin da yakawomu wurin ka da daddaren nan" ya sakeyin shiru sanan ya numfasa yace "shi so hallitan ubangiji ne, danhaka so gaskiya ce hakama ki, Alhaji d'ana yazo gidanka jiya sai cikin iko irin na Ubangiji yaci karoda yarka Du'a kuma Allah ya jarabceshi da sonta ainun aranshi danyau haukace mana kawai ne baiyiba ga kannina nan katambayesu kaji, yace shiyabarma Nana duka abubuwan dayamata amman yafasa aurenta dan baya sonta Allah yahadashi da Du'a ita yakeso itakuma yakeson Ya aura inhar ka yarda zaka bamu" tunda suke maganan Abba yake kallonsu babu ko kyafta ido, yakai kusan minti biyar ahaka baice komiba dakin tsit kakeji sanan yay gyaran murya yace "to Alhamdulillah naji dadi yanda kukazo kukasamen, shi gaskiya dayace koda batada dadin ji, naji dadin yanda kuka sanardani gaskiya batare da kwana kwana ba ko kuma boyeboye ba danhaka nima zan sanardaku gaskiya Alhaji" yay maganan cikin mugun hikima da ilimi sanan yace "it's very okay idan danku Muhsin yaji bayason y'ata bazai aureta ba shi aure daman yagaji haka ko anyi ana rabuwa, amman gaskiya itace bazan iya bama Muhsin wacce yaji yakeso dinba wato Du'a" dasauri Muhsin yadago kanshi yakalli Abba idanunshi sunyi jaaa sosai. Abba yacigaba. "Alhaji kai mahaifine haka nima mahaifine, yanzu wani yazo yana tareda yarka har a kusa bikinsu sai yaga kanwarta yace yafasa aurenta kanwar yakeso zaka yarda kabashi"? Abba yamai tambayan shiru Baban Muhsin yayi yakasa amsa tambayan, Abba yace "duk wani abinda zai raba kan y'ay'ana ko family na bazan taba yinshiba, gwara afasa auren gabadaya da inbaka wata, dan haka I am sorry idan maganata ko amsata bata kuma dadi ba amman bazan iya baku auren Du'a ba, as for kayayyakin dakuka kawo duka in sha Allah zamu aiko muku dashi, Allah yasa hakan ne yafi alkhairi" Kafinma Baban Muhsin yayi magana Muhsin ya rarrafa da gudu zuwa gaban Abba, kneeling yayi yahade hannayenshi biyu muryanshi narawa kaman wanda zai fasheda kuka yace "Abba Abba wlh wlh wlh na rantse da Allah bawai dan cin mutunci ko toxarci kodan inci zarafin Nana nai hakaba, wlh kawai Abba azuciyata naji bana sonta wlh tunda nasa Du'a a idanuna nake so ko kulkewa nayi saina ganta, Abba kataimakamin dan Girman Ubangiji" tunda yake maganan daga Abba har Hamad kallonshi sukeji, ahankali Abba yasa hannayenshi yakama hannun Muhsin dayake rokonsu dashi yace "Son kayakuri kotayaya zaka roken I don't think I can risk my family for this, I can't stand naga kan family na ya rabu sabida one bad decision dazanyi ba, bazan iya baka Du'a ba, it's final" to Abba biggest suprise kawai yaga Muhsin yafashe da kuka sosai, daura kanshi yayi kan cinyan Abba cikin kuka yace "Abba wlh idan baka bani Du'a ba zan iya mutuwa dan Allah kayakuri, I am sorry if I hurt you sabida nace banson Nana...." Iyayenshi kasa koda motsi sukayi, sunsan Abba made the right decision dankosu basuso sunzo ba mugun so da gatan dasukema Muhsin dinne yasa sukazo su gwada luck dinsu. Ganin yanda Muhsin ke kuka yasa zuciyan Babanshi yafara breaking shifa baida wanda yakeso kaman Muhsin aduniyan nan, kallon Abba yayi yace "Alhaji name anything dakakeso wlh zan maka indai zaka bama dana Du'a dinan dayakeso, kaga wlh zan iyasa acireka daga matsayin HOD dinan abaka Deen na BUK gabaki daya, idan bakaso zan baka aiki akasan waje, wanan gidan na chanza maka nabaka lafiyayyen gida anan GRA kano, mota kudi koma mekakeso just name it zan baka inda zaka hakura kabama yarona wacce yakeso kaganshi nan shikadai gareni kataimakamin please" sake tashi Muhsin yayi daga jikin Abba fuskarnan nashi hawaye ya wankeshi yahade hannayenshi yana kallon Abba, dan murmushin manya Abba yayi yace "I am happy da position da dukiyan da Allah yamin a rayuwa bana bukatan kari, nariga nayi maganata idan babu matsala zan haura sama inada y'a mara lafiya naduba, Hamad you can see them off okay" gyadamai kai Hamad yayi Abba yatashi, sosai Muhsin yafashe da kuka, kanin Baban Muhsin Alhaji Mubarak yatashi yay wajen Muhsin yace "Kato dakai kana kuka, ga matanan agari kaman ledan pure water kodaga kasan waje kakeso kayi aure Babanka zai auromaka tashi mutafi" kintashi yayi saifada sukayi da gaske suna dagashi sanan suka fitardashi daga falon Hamad yatashi yarufe kofa jikinshi a sanyaye. koda Abba yatafi sama dakinsu Nana yabude yashiga, bin kowa nadakin yayi da kallo Nana na kwance kaman mara lafiya idanunta a lumshe sai Hawwa ce idanunta biyu, tana ganin Abba tace "sannu da zuwa Abba" gyadamata kai kawai yayi yakalli Du'a dake barci har lokacin sanan yajuya yafice yakoma dakinshi, ko zama baiyiba Mum tabude kofa tashigo dakinshi, juyowa yayi yakalleta sanan yazauna akan kujera yana ganin idanunta kadai yasan taji duka maganganunsu a falo dan idanunta sunyi ja kaman ma hardan kukan bakin ciki tayi. zama yayi kan kujera yana kallonta, daurewa tayi tahadiye abinda ya tsayamata arai tace "yakukayi dasu Alhaji" jaridan shi dakekan table yadauka ya gyara zamanta akan hannunshi sanan ya kalleta yace "idan Allah yakaimu gobe duk wani abu na gidansu Muhsin ki tattarasu tass zansa azo adauka amayar musu" wani irin faduwa da rawa gabanta keyi dan babu kalan burin dabata dashi akan auren Nanan ta da Muhsin, finally yarta zatai rayuwa gidan masu kudi shine tashi daya kaman aradu zancen aure yamutu, daurewa tayi tace "does that mean babu zancen aure? Ba za'ayi auren Nana da Muhsin ba kenan?" bude jaridanshi yayi zaifara karantawa yace "eh babu zancen aure, Allah yabata wani mijin nagari" yay maganan tareda gyara zama kan kujera yana karatun littafin shi dakyau sosai take kallonshi jitake kaman tarufeshi da duka tsabagen bakin ciki, wai ace anfasa auren yarsu 26yrs finally year student din yarsu, yarinyar dayasan tanason Muhsin dinta yau all of a sudden amman this guy is still acting kaman it's nothing, jitayi idanunta sunjuya sama wutan bala'i nacimata zuciya tajuya fuuu tafice ko tsayawa kulle mai kofa batayiba tana fita tacikaro da Hamad daya hauro sama zaizo yaduba Du'a, idanunta kadai yagani yasan ba lafiya hakan yasa yajuya dasauri zai koma dasauri cikin mugun ihu tace "dan ubanka wlh katafi saina tsinemaka albarka agabanka aka fasa auren yarka bakai komi dan taimakon lamarin ba dawonan" juyowa yayi ahankali sanan ta shiga kwalama yaranta kira. "Amal Asiya" dasauri suka fito daga dakin su harda Aneela yar Mami, jin ihun Mum tasa Mami itama tafito, kama hannun yaran tayi tawani irin tura kofan dakin yaran, yanda kofan yay mahaukacin kara yasa Du'a ta firgita sosai ma tabude idanunta, shigowa Mum tayida Hamad da Amal da Asiya, sanan ta kalli Nana da Hawwa daduk ita suke kallo tace "Nana saurareni kiji anfasa aurenki, Muhsin har kuka yake yakama kafan ubanki yana roka abashi wanan yar Aljanun" tanuna Du'a, dasauri Hamad yace "Mum please stop all this bahaka ake handling situation like this ba sokike zuciyan Nana yabugu eh"? Cikin bakin masifa Mum tace "buguwa na nawa kuma" tasake juyawa takalli Nana da kallonsu kawai take kaman gunki tace "Nana Muhsin yace bazai aureki ba yanzu haka ubanki yace ahada komi nasu harda akwatin dasuka kawo naki amaidamusu abinsu gobe dasafe" kokarin yunkurowa take tatashi tasauko daga gado kawai jiri yadebeta ta yanke jiki zata fadi dawani irin sauri Hamad yatareta yace "Nana Nana" juyowa Mum tayi takalli Mami data tsaya daga bakin kofan tana kallonsu kawai saitaikan Mami shakumo Mami tayi tace "wlh saina kasheki duk abin nan dake faruwa dadi kikeji yarki ta kacema y'ata miji har celebration kike kikaji Babansu daki kina cinshi da rana tsaka" ganin Mum ta shako Mami yasa dasauri Hamad yasakinma Hawwa Nana yatashi daga Du'a har duka yaran kuka suke. "Hajara!!!" Abba yakira Mum da mugun karfi daidai lokacin da Hamad ke cire hannunta daga wuyan Mami datahau tari sosai, Abba cikin fushi yace "tattara yinaki yinaki kibarmin gidana" wani kallo tamai tace "naji zan barmaka gidanka amman wlh saidai nabar gidan da daddaren nan da yarana duka dan bazan taba barinsu da wanan yar Aljanun dakuke raina agidan nanba dansaita hana yarana aure" cikin fushi Hamad yace "Mum wai what is all this eh haba Mum? Auren Nana has nothing to do with Du'a kawai Allah ya kaddara ba mijinta bane, kidena kiran Du'a yar aljanu, Mum this isn't right mekike koyama su Hawwa ne, haba Mum haba" nuna kanta tayi tana kallonshi tace "ni kake gayama magana Hamad eh" saikuma tafashe da kuka tace "kana gani sabida Du'a anfasa auren kanwarka sanan kace babu ruwanta ba laifinta bane, kanwarka tasami miji gidan arziki gidan hutu kasan gwalagwalai nawane aka samata a akwati eh, har mota ya siyama Nana ranan da aka kaita yace zai bata yarinyar chan tai amfani da tsafin jikinta ta kwacema kanwarka miji kace kaza kaza, nagode Hamad" tashi tayi ahankali tana kuka sosai tawuce tashiga dakinta, zama dirshan Mami tayi akasa takife kanta akafafunta, ahankali Abba yatako yashiga dakin Nana yakalla da Hawwa ta yayyafama ruwa ta farfado sosai take kuka shiru kawai yayi saiyajuya, Du'a yakalla data farka itama tana kuka sosai tana goge idanunta da bayan hannu, fice wa kawai yayi daga dakin. Ranan banji akwai wanda yayi kyakkyawan bacci agidan ba. Karfe 7:30 Abba yasauko kasa Mami ce kadai a dinning tana hada kayan breakfast, bamataji tafiyanshi ba dan aiki take amman tayi mugun nisa a tunani, binta yayida kallo saikuma ya ijiye jakan aikinshi kan kujera yataka har zuwa dinning Mami bataji zuwan shi ba, hannunshi yakai yakama nata firgigit tafarka tareda juyowa bin fuskanta yayi da kallo idanunta ja da alamun tasha kuka, murmushi takakalomai sanan ahankali tace "ina kwana harka sauko" bai amsa gaisuwantaba yace "tunanin mekike"? kaman bazatai magana ba but ganin yanda ya tsareta da idanu yasa tace "tunani nake kodai mu aika Du'a wajen Mama nane" tsareta yayida mayun idanunshi ya dayasa kawai taji tacigaba da magana tace "Dadyn Hamad understand me kaga sabida Du'a gabaki daya gidan nan babu lpy, Nana tabani tausayi Allah kadai yasan what she is going through wlh is not easy karasa masoyinka, look at Mamansu ga Hamad, in order for peace to rain ni ina tunanin mukaita wajen Mama tai zamanta achan har Allah yasan yanda zaiyi da ita, daga saukanta kasa jiya jibi kalan trouble datajawo" murmushi yadan mata yace "fitanta so daya yajawo wanan matsalan idan muka kaita wani wajefa da bamanan, kinmanta komi ne tun yanzu"? Ajiyan zuciya tasauke takasa magana, murmushi yayi yace "bani abinci inada meeting by 8" gyadamai kai tayi tashiga serving nashi abinci, abincin yashiga ci wayanshi tafara kara ajiye cokalin abincin yayi sanan yatura hannunshi cikin aljihu yaciro wayan ganin mai kirannashi saida kirjinshi yadan buga amman yadaure yakai wayan kunne zaiyi magana aka katse shi. wani sharp muryan tsohuwa ce kemagana ta wayan. "nasan yau litinin ko ubanme kakeyi kowani kalan aiyyukane kakeyi kabarsu Shafi'u ka tattaro iyalinka tatas banda wanan yar Aljanun kutaho Ikara yanzun nan" tana maganan ta katse, ahankali yazame wayan daga kunnenshi yay jimmm yana kallon Mami da ahankali tace "Kaka ce?" gyadamata kai yayi yace " jeki shirya yara kowa yafasa zuwa school Ikara zamu yanzu" bude kofa akayi Ahmad yashigo yanasanye da kayan sojoji kafinma ya gaida Abba Abba yace "Ahmad get ready we are going to Ikara" shi kanshi Hamad din baikara fadin wani abubu, saukowa sukaga Mum tayi taci gayu itada yaranta da Nana da idanunta sukai ja sosai tace "mudai mun shirya" ahankali Mami tabi ta gefenta tai sama kaman zata shiga dakinta saikuma tabude dakinsu Du'a ta shiga, zaune taga Du'a kan gado, duka kumburin da fuskanta yayi sun sabe dan dama nan da nan ciwo ke warke wa ajikinta sai idanunta dasuka kumbura sosai, ganin Mami tashigo dakin yasa tabude baki zatamai Mami magana dasauri Mami tajuya tafita dakinta tashiga tadauki hijabi sanan ta tattaro kansu Muhammad da Aneela suka fito, a falo suka sami kowa Abba yace "mutafi" juyawa yayi yakalli Uwani data fito daga kitchen yace "ki kulada Du'a ki kaimata abinci sama zamuje kauyen Ikara" gyadamai kai tayi tace "Allah kiyaye hanya agaida Hajiya" fita dukansu sukayi Mami tadan juyo hada Pido tayida Du'a data fito daga dakinsu ta labe asama idanunta sun cikoda kwalla, Sakai tayi tafice dasauri. 💫 KYAWUNA JARABTA 💫 ✍️ M SHAKUR Free page EPISODE 7️⃣ Tashi tayi ahankali tawuce cikin dakinsu bathroom tashiga wanka tayi da ruwa mai zafi sosai hakan yasa taji duk wani ciwon jikin datake ya watsake sanan tadauro alwala tafito daureda towel, maita shafa ajikinta sanan tabude wardrobe din, wani dogon riga kawai taciro na atampa ja ta shirya cikinshi sanan tasaka hijabi tai salla, zama tayi wajen kan dadduma hakanan kawai gabanta yake fadi maisa tunda ta taso tafara wayau rayuwanta kecikin kunci eh? Maisa ita kadaice problem din gidan nan, Kakanta bata sonta sabida itama tadaina zuwa gidan danta Abban su, Abba baya sonta kawai ijiyeta yake sabida bazai iya koran y'arda ya haifa ba, Mami ma kaman kunya takeji ace ta haifeta, gabaki dayan mutanen datasani aduniyan nan mutum biyu ne tasan kawai suna sonta Nene Maman Mami wacce ita dinma tun tana yarinya ne Mami ke daukansu suje su gaidata tunda Abba yahanata fita ko'ina bata kara zuwa gidan ba saidai ta aikomata da kayan kwalama idan Mami dasu Aneela sunje kokuma musamman takira Mami taita mata masifa sanan tasaka Mami tabata waya su gaisa da Nene. Maisa iyayenta da yanuwanta basa sonta? duk sabida wanan kamannin nata to ita tayi kanta ita tayi kanta eh? share hawayenta tayida sauri jin anbude kofan dakinsu, Uwani ce tashigo tace "kin idar kyakkyawan gidan nan, zokiyi karin safe" tashi tayi ahankali tazo inda Uwani ke nunamata, zama tayi Uwani ta ijiye tray abincin agabanta tace "oya ci abincin ki, Allah zai sakamiki, Nana takamaki tadinga jibga danma baki iya rashin kunya bane dakin biyemata kunyi damben da kyau, yi breakfast kyakkyawa" all maganan nan da Uwani keyi bata kalleta ba saida tai maganan karshe sanan tadagokai ta kalleta lumshe ido tayi tabude cikin yar muryanta tace "dan Allah dagaske ni kyakkyawace" zama Uwani tayi akasa kusada ita tana kara kallonta opportunity kaman daman abinda take jira kenan tace "ai wlh Du'a kinada bala'in kyau da duk yan nan gidan babu mai kyanki, kina kama da masuyin film din kasan waje, ai saisa yan uwanki kejin haushin ki sabida kin fisu kyau ga wanda Nana zata aura nan jiya daga ganinki yardage keyakeso, jiya ina kitchen ina jinsu wlh harda kukanshi wiwi sabida ke, ki godema Allah kawai" murya chan kasa tace "ni banson kyau nafison nazama kaman kowa sabida yan uwana da kowa su soni, banson yanda nake rayuwa ni kadai ban iya komiba" dasauri Uwani tace "ko yanzu ma suna sonki ingayamiki kawai bakin ciki ke hanasu nunawa" shiru tayi tana kallon abincin batareda ta tababa, Uwani dabata gaji da kallonta ba tace "yanzu dasuke kulleki adaki haka basuso ki sami naki saurayin kiyi soyayya kiyi aure ne" dagokai tayi takafe Uwani da idanu batare datace komiba, dan murmushi Uwani tayi tace "tashi muje falo abinmu yau mu kadai agida mu sakata mu wala". "Salamu Alaykum" sukaji an kwada sallama dasauri daga itahar Uwani suka ware ido, Uwani tace "tashi muje falo muji mene mai gadi kenema wajenmu" tai maganan tana daukan tray abincin ta, tashi tayi ahankali sanan tabi bayan Uwani suka sauka falo, abincin ta ijiye mata akan table sanan takalleta yanda take tsaye kusada Uwanin tace "oya zauna kifaracin abincin bari na sauka naji maisa Bala mai gadi kemana sallama ina zuwa" gyadamata kai tayi tazauna ahankali sanan tadauki plate din nama tadaura akan jikinta tafaraci, bude kofa Uwani tayi mai gadin su tagani tareda Muhsin dake sanye da wasu hadaddun kananun kaya masu bala'in kyau yasaka glass a ido baki, ware ido tayi zatai magana dasauri mai gadi yasa hannunshi akan lips dinta alamun tayi shiru kartace wani abu, sanan ya matsa ta gefenta yajawo kofan falon yarufe batare da Du'a ta ganshi ba danta gefe ya tsaya yajuyo yakalli Muhsin yace "minti daya yallabai bari nai magana da ita" gyadamai kai Muhsin yayi tareda tabe baki shikuma ya yafito Uwani alamun tazo, binshi tayida saurin zuwa gefen daya tsaya tanason taji me wanan Muhsin din dataji anyi baran baran dasu jiya kenema kuma agidan nan, tace "me wanan keyi agidan nan Bala"? dasauri Bala Maigadi yace "yanda kika ganshi haka nima naganshi, ashe tun asuba yana anguwan nan akan idanunshi su Alhaji suka tafi Ikara dazu" dasauri tazaro idanu tace "yoni nabani, daga ganin sarkin fawa waisai miya tayi zaki, dagaske yakewai Du'a yakeso, tome yazo yi yanzu"? dasauri Bala Maigadi yace "soyake mudan bashi dama yaga Du'a ta hanyar barin gidan nan na minti talatin kadai" zaro idanu Uwani tayi tace "kai Bala hauka kake eh, ba amananta aka barmana ba, me zamu barshi dagashi sai ita yarinyar dakasan babu abinda ta i......." kasa karasa maganan tayi sabida wata bakar jakan Viva bag dataga ya tsugunna yadauka sanan yazo gabanta bude mata ledan yayi wani irin zaro idanunta datayi zaka dauka idanun zasu fadi kasa ne sabida uban kudin datagani cikin ledan, dasauri yace "miliyan biyar ne anan inhar mukamai abinda yakeso tamuce halak malak, zandauki miliyan uku nabaki biyu, aikin shekara nawa zakiyi agidan nan baki sami miliyan biyu ba duka duka albashin naki da dubu goma sha biyar ne, arziki na kiranmu jibi uban kudi haka namune kawai idan muka bama mutum minti talatin kachal, kina ciki ko baki ciki?" dawani irin sauri ta hadiye yawu harsaida yay gut tace "ina ciki wlh Bala" murmushi yayi yace "bari nakai kudin na boye adakin saimu tafi" gyadamai kai tayi yawuce itakuma tadawo inda Muhsin yake tsaye tace "yallabai ko awa dayanema kayi bakada matsala damu, jiyama ingayamaka saida Nana tamata dan banzan duka su basusan shi so Allah kesawa ba, ga yarinyar danya jagab nunan inuwa bamatasan Yaya ake dambe ba, bafata fita bamatasan Yaya zafin rana yakeba" daidai lokacin Maigadi ya iso yakalleta yace "mutafi" gyadamai kai tayi sanan ta kalli Muhsin tace "tana zaune a falo tanacin abinci, Allah baka sa'a" yatsine fuska yayi dan matan disgust him sosai sanan yajuya yana kallonsu suka wuce suka fita, Bala Maigadi yasa key tawaje suka wuce abinsu suka zauna kan wani benci dake facing gidan ta dayan bangaren hanya. Ahankali yasauke ijiyan zuciya tareda fuzarda iska he can't wait to set his eyes on her again, haurawa yafara yi kan matattakalan benen sanan ya tsaya jikin kofan yakai hannunshi knocking yayi ahankali, tanacin nama taji anyi knocking dasauri takalli kofan kaman mai tunani toko Uwani takasa budewa ne tawaje, tunanin haka yasa ta daukan last meat din dake kan tray din a hannu cikin yar muryan nan nata tace "ina zuwa" sanan takarasa wajen kofan hannu daya tasa tana bude kofan dayan hannunta kuma na bakinta yana kokarin gutsiran nama da duka hankalin ta kekai wani kamshi daban yawani mata sallama a hanci dayasa dawani irin sauri tadago idanunta takalli gaban kofan dan tasan Uwani banda kamshin kitchen din gidansu babu wani kalan kamshin datakeyi, dudda yasa glass hakan bai hanata ganeshi ba Muhsin ne yay wani irin kyau cikin kananun kayan dayasaka na jeans da t-shirt black duka, yasaka black eye glasses a idanu, tundaga kan fararen yatsun kafanta yake kallonta har zuwa thick thigh dinta da wanan flat tummy da kirjinta dakenan acike wanda kallo daya yamusu yasan ba tasaka bra ba dan is so obvious acikin just simply gown din datai throwing ajikinta bayan tai wanka datai salla zuwa fuskanta dahar yanzu bai gama washewa ba da gashinta dakenan a bude tai parking dinshi jelan na yawo ga hannunta dake kan bakinta dake rikeda nama idan kaganta zaka dauka yar wani president na all this Arab countries ne tsaban kyan da Allah yayi awurin, Muhsin jiyayi cikin jikinshi internal organs dinshi na kyarma sabida ganinta, da kyar yadaure yazare glasses dinshi daga idanunshi yakalleta tareda sakin mata wani cute smile yace "Hi Pretty" ahankali tasaukar da hannunta dake rikeda nama kasa sanan tadauke kanta daga kallonshi tace "Ya Nana batanan sunfita dasu Abba" takama kofan zata tura dasauri yarike kofan gam yana kallonta, sake kokarin tura kofan tayi da duka karfinta amman takasa hakan yasa tadan kalleshi tace "I said Ya Nana is not around leave I want to close the door" turo kofan yayi yashigo dakin dasauri takoma baya yace "I come to see you Pretty ba wajen Nana nazo ba, wajenki nazo Du'a cus you've stole my heart". 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 8️⃣ Ganin yanda dukta firgice da maganan dayayi yasa yace "okay bari natafi tunda kece kawai stealing zuciyata ni banyi naki ba gashinan is obvious baki sona natafi" juyawa yayi kaman zai fice daga dakin bata ankaraba kawai taji yawani juyo ya rungumeta tsam tsam yarage tsawon shi ta hanyar sanya fuskanshi a wuyanta yana shakan kamshin natural fatan ta that smells innocent irin smell din da yaran da basusan maza ba keyiba, innocent children smell dayasa yaji yana neman ya kwarkaance, wani irin ihu tayi jikinta narawa sosai jin namiji ajikinta. "wayyooo innalillahi Mamiii" murya chan kasan makoshi yana kara shinshinata kaman yanda dan biri ke shinshina bishiyan ayaba yace "stop screaming babu wanda zaijiki, dagani saike agidan nan I love you sosai Du'a, Du'a please ki saurareni nazo muyi magana ne mai bala'in mahimmanci" wani irin yanda gabanta ke faduwa harjitayi kaman numfashinta zai dauke, kokarin tureshi take takasa sake matseta yayi ajikinshi sanan ahankali yace "kizo mugudu nafitar dake daga Nigeria muyi auren mu mu more life, me kikeyi agidan nan? You don't deserve this life da treatment din nan da akemiki agidan nan, kinsan darajanki kuwa? sunyi depriving naki education, bamaku dakudi jibi gidanku kaman gidan kajinmu, I Wil give u money da dadin duniya da komi nawa I am telling u, I will forever spoil u Du'a" fashewa da kuka tayi sosai bamatasan mezatayi ba dan magana yake kaman wanda yahaukace tace "ni bana sonka karabu dani, babu ruwana dakai, kai saurayin Ya Nana ne kadena min magana, Uwaniiiiii" takwalama Uwani kira da duka muryanta jikinta na bari sosai, ahankali yasaketa yana rikeda hannunta gam gam ya tsaya yana kallonta yanda take goge hawayen idanunta tana kallon kofa tana kiran Uwani, tundaga kan kwayar idanunta yake kallo shi kanshi kaman zai kurma ihu yakeji akanta he just want this beautiful pretty yar India yarinyar nan in his possession, wanan yasameta yanda zaima abokanenshi gayu da itaba aiharsaisun fara kishi dashi, wani irin bin wuyanta yayi da kallo fari gashinan smooth zuwa kan kirjinta dake cikin rigan babu bra akansu kokarin fizge hannun datakeyi yasa nonon suna wani irin rawa suna girgiza da tumbutso, gasu a mugun tsaye wani irin kankancewa idanunshi sukayi wani kalan sha'awanta suka shigeshi kaman yay gahoda ita yacita anan yakeji, wani irin finciko hannunta yayi hakan yasa tawani kalan fadi kirjinshi da karfi boobs dinshi sukai slapping chest dinta wani wahalallen kara tayi. "wayyo na shiga uku" wani irin lumshe ido yayi yana kara danno bayanta da dayan hannunshi yace "Du'a nadade banga macen da Allah yama gata irinki ba, Allah yamiki nono mai kan tasa zakibani nasha su" wanan karan fashewa da kuka sosai tayi jikinta nabari. "Uwani, Uwaniiiiii kina ina" yanda tafashe da kuka sosai abinma wani irin Dada karamai shauki yake dasauri yakai kanshi zaidaura awuyanta. "nooo" tai ihu sanan tai kasa zata duke biyota yayi kasa zai rungumeta da duka kafafuwanta guda biyu tawani turemai mara tahada da dick dinshi ta ture duk batasani ba wani irin kara yayi sanan yarike dick dinshi gam yana cizan lips da mugun sauri ta tashi tawani yi kofa tafice da gudu ganin haka shima yabita dagudu yace "zonan ina zaki" hanyar gate dinsu tayi tana kuka tana waigen baya jijjiga gate din tashiga yi tana kallonshi yanda yataho yana murmushi yace "I told you the gate is locked it's just me and you now" ganin yataho kanta gadan gadan yasa tawani kwasa da gudu shima yakwasa da gudu yana binta abaya tana waige, ganin ta dunfari rijiyansu dayagani abude ba'a rufe marfin ba kuma from look of yanda take waigoshi tana gudun atsorace bamata lurada rijiyanba yasa yace "stop there, bazan miki komiba Du'a, riji........." kafin yama gama maganan tafada rijiyansu tsundum dasauri yakarasa wajen rijiyan ya leka, rijiyan zurfi gatada duhu, rawa jikinshi yafara baisan lokacin daya shiga ciro wayanshi daga aljihu ba dialing number mai gadi yayi saida yay ringing sanan yakatse sanan yajuya da saurinshi yay gate, daidai lokacin aka shiga bude gate din, aka turo aka shigo Bala Maigadi ne tareda Uwani sunamai murmushi Bala yace "ai bamaka gama cin minti talatin....." kafin yama karasa maganan Muhsin yanuna musu rijiyan dakenan abude yace "tafada rijiyan ku......kuc....I...rota" yana maganan yabita gefensu dasauri ya fita ya shiga motanshi yaja yabata wuta yabar anguwan, atare Uwani da Bala suka kalli juna saikuma suka kwasa da mugun gudu sukai wajen rijiyan atare suka leka ganin ruwan na rawa ana tumble tumble yasa cikeda tashin hankali Bala yace "fita waje ki nemo mana taimako yarinya tafada rijiya dan ban iya ruwaba ko kadan, innalillahi wa innailaihi raji'un, bari nadauko igiya na zura mata yi sauri" dawani irin gudu takwasa waje, fara wangale gate din tayi gabaki daya sanan tashiga ihu a anguwan nasu dababu wasu jama'a sosai. "jama'a ataimaka mana yarinya tafada rijiya, jama'a ataimaka mana yarinya tafada rijiya" kafin kaceme matan makota sun soma fitowa ana shigowa gidan, gashi kaman anyi baki duk babu maza a anguwan kowa yatafi nema dan dama anguwan sabuwa ce kumababu mutane sosai. Gida yacika fal da matan anguwan ana salati ana sallallami, Bala Maigadi har zufa yake yana zura mata igiya yana ihu yace "Du'a ko yayane kifito da hannunki sama ki chapke igiyan zamu jawoki waje" wata mata dake kiran mijinta awaya tace "wanda yafada ruwa fa bayajin magana nataba fadawa rijiya, ji zakiyi ruwan na shakeki, ayita salati kawai idan tanada kwaran kwana zakuga Allah zai kawo yanda za'a ciro ta, Baban Nana nake kirafa ya iya ruwa kuma shagon shi nabaki titi amman baya dauka".......... THIS BOOK IS 500 U CAN PAY INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK SAIKI TUROMIN EVIDENCE OF PAYMENT TA WATSAPP NUMBER 07012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR Dan chatting dina ni M Shakur directly click on this link wa.me/+2347012181461 Free page EPISODE 9️⃣ Wata latest AMG Benz ne fara ta doso cikin anguwan tana tafiya ahankali sabida tudu da kwarin anguwan yasa motan bazata iya tafiya dagudu ba, mutane biyune acikin motar, wani farin guy ne bala'in kyakkyawa da akalla zaikai 33yrs ko 32 yana sanye da jumper na wani classic USA yard dakenan da bala'in taushi blue, ba'ama dinki aiki ba amman yahadu yana tuki da hannu daya yanashan horse power da dayan hannun, saikuma wani black guy hadadden gaske dakeda kakkauran jiki lebenshi pink sosai yana zaune abaya da akalla zasuyi agemate damai tukin, yana sanye da suit shima mai ruwan toka da necktie awuyanshi yadaura Mac book kan cinyanshi yana dadannawa, yanada wani irin cikan coily gashi akanshi dasuka nannade sosai yayi kama da black somalian guys sosai looking damn sexy and hot, irin definition of classic young rich guy dinnan. "wai dagaske ka maidani drivern ka ko Asad" dan dagokai yayi yakalleshi saikuma yamaida kanshi kan laptop din yacigaba da abinda yakeyi batare daya kulashi ba, dan tsaki mai tukin yayi murya chan kasa yace "mtsww this guy piss me off kodayaushe" batare daya kalleshi ba har lokacin kanshi nakan system din dayake aiki akai yace "and he heard u loud and clear Sharif" dan dariya direban da aka kirada Sharif yayi yadan waigo yakallehshi ganin hankalin hi nakan aikin dayake yasa yajuya yamaida hankalinshi kan hanya daidai lokacin kuma yataka wani irin mahaukacin burki da saida yasa Asad dake baya kanshi yabugu da kujera laptop dinshi yafadi akasa dasauri yadago kanshi danshi yadaukama wani abu suka taka suna neman suyi accident ne Sharif yaci burki kawai dukansu biyu sukaga Uwani gaban motansu takife kanta akan glass din motan tana kuka sosai tahade hannaye, kallonshi Sharif yayi dasauri Asad din yace "is she a kidnapper"? Dasauri Sharif yace "how am I suppose to know eh? Ammi saida tace inzo da security indaukeka kace kai bakason azo daukanka da kowa, yanzu in kidnappers ne Yaya zamuyi"? daidai lokacin tarinmata kusan su shidda suka fito daga gidansu Du'a da gate kenan abude, Babban cikinsu ne ta bubbuga motan dan tinted class ne tagefe dasauri Asad yace "don't open the door" bude motan Sharif yayi yafita ganin matan aure kamilallu, Matar tace "Malam dan Allah kataimaka mana kakap anguwan nan babu maza yarinya kuma tafada rijiya kusan minti takwas da rabi kenan bamu samu nasaran ciro ta ba kuma iyayenta basa nan sunje kauyen su chan Ikara dan Allah kataimaka mana maganan rai ake anan" shiru Sharif yayi yana kallonsu saikuma yakalli gidan dasuke nunamai yanda aka taru yara da manya gawasu na kuka dan abin abin tausayi yasa yace "Ina zuwa" shiga motan yayi dasauri yakalli Asad dake binshi da kallo yana jiran bayani yace "Asad zomuje muyi taimako" dasauri Asad yace "taimakon mene" dasauri yace "yarinya ce tafada rijiya and parents dinta are not around tayi about 8min a rijiyan kuma kasan ni ban iya ruwaba pls muje kacirota" Wani kalan matsiyacin kallo Asad yamai yace "you must be joking, na iya ruwa yes na iya ruwa kataba ganin na shiga rijiya ne? I don't think namataba ganin rijiya, common key this car mubace daga anguwan nan" dasauri Sharif yace "common Asad maganan rai akefa anan what if yarinya tamutu right before our eyes when munada chance na saving life dinta mezamu fadama God" maida kanshi yayi jikin kujera yace "sannu superman, tunda kanada relation ne da yarinya ai kaje kai saving nata nidai count me out" dasauri Sharif dake kallonshi cikeda mamaki yace "haka kace" tabe baki yayi yace "saikuma kayi" yay maganan yana lumshe ido danshi bacci ma yakeji fita daga motan Sharif yayi yakalli matan yace "muje ingani" dasauri daga Uwani har sauran matan sukai gidansu Du'a tareda Sharif din dake biyeda su, almost 1min yayi idanunshi a lumshe saikuma yabude idanunshi dasauri yajuya yakalli gate din su Du'a, wani irin banzan tsaki yayi sanan yabude kofan bayan yafito yana maida kofan yarufe yace "you are messing with my mind Sherif" sanan yawuce ahankali yabisu, kafanshi nadama yasa yashiga gidan wani irin sanyi yaji yay wani irin cringing acikin bones nashi dasauri ya tsaya chak yanabin duka gidan da kallo yanda yaga duka matan gidan sun juyo suna kallonshi kaman sunga wani hero ko celebrity na movie, juyawa yayi dasauri zai fice daga Gate din yaji muryan Sharif yace "yauwa gashinan yazo, the well is here Asad" dasauri yajuyo yakalli Sherif din dake gaban rijiyan kusada Bala direba yana nunamai rijiyan, wani kallo yama Sherif irin zamu ganmu dinnan sanan yashigo cikin gidan zuwa gaban rijiyan, necktie dinshi yacire yabama Sharif din yakarba, sanan yacire takalminshi dakuma jacket dinshi, igiyan dayagani hannun Bala ne ya karba wani irin dauri yama igiyan a waist dinshi da sanan ya kallesu yace "zan shiga ciki idan Nagano ta zan muku sign ku jawota" duka gyadamai kai akayi, juyawa yayi yakalli rijiyan baitaba shiga rijiya ba, kallon Sharif yayi dake kallonshi irin kallon nan na u caused all this sanan yay wani irin tsalle yafada rijiyan jikake tsundum.!!! Leka rijiyan dukansu sukayi Bala yace "kace ya iya ruwa sosai ko" gyadamai kai Sharif da kirjinshi ke dukan uku uku yayi yace "eh ya iya amman baitaba shiga rijiya ba" wani irin salati duka gidan aka dauka, wata mata cikinsu takalli Bala tace "incedai ka kira mahaifinta ka sanarda su inma barin ikaran nan subaro sutaho fa dan wanan yarinyar inhar ta rayu to Allah yace kawai kwanan ta nagaba ne" ahankali Bala yace "nariga na sanar dashi" "jama'a Qulhuwallahu kafa bakwai" nan aka fara karatu fa, ganin yayi kusan 2min a ruwan ruwan ma yadena motsi yasa dasauri Sharif ya tsugunna yana leka rijiyan. "Asad Asad can u hear me are you okay? Asad" kana ganinshi kasan hankalinshi atashe yake, kusan 20sec dagama kiranshi saigashi yawani bullo da kanshi daga ruwan yay ihu yace "I got her!" dasauri daga Sharif har duka yan gidan sukahau hamdala, dasauri Sharif yace "what about u are you okay Asad" yana kokarin janyo Du'a kanta yafito daga ruwan gabaki daya yace "we will talk about that when am up there" cirokanta yayi daga ruwan sanan yadaura kanta akirjinshi ya rungumeta ahaka, igiyan dake waist dinshi ya shiga warwarewa sanan yadaura shi kan waist dinta duk acikin ruwan dan kansu ne kawai ke sama sanan yace "Sharif I don't know if she's still alive but she is unconscious, na daura igiya a waist dinta, ni zan dingabin matattakala while am holding her kukuma kunajan igiyan waje am I clear" dasauri Sharif yace "yes Asad sanan yatashi dasauri yarike igiyan tagaban Bala yakama ta bayanshi sanan yacilla matan ragowan igiyan yace kuyi layi ku kama igiyan mujawosu waje, duka rike wa sukayi Sharif yace "give us go ahead we are read Asad" hawa matakala daya Asad yayi yana rungume da ita har lokacin sanan yadago kanshi yakalli sama yace "pull us Sharif" jawo igiyan suka shiga yi yana rikeda ita yanabin matattakala har sukakai sama Tsugunnawa Sharif yayi yamikamai hannu da taimakonsu yafito rikeda Du'a akan kafadan shi sanan ahankali yacirota daga kafadarshi ya shinfidar da ita akasa sai alokacin yamaga fuskarta yanda yake kallonta haka kowadake compound dinan ke kallonta, Uwani ce ta rarrafo tana kuka sosai tace "mun shiga uku mun lalace Bala ta mutu jibi yanda takara haske, Innalillahi wa innailaihi raji'un" ahankali Sharif dake gefen Asad yace "Asad tamutu ne"? "I dont know" Asad yabashi amsa atakaice yana dauke idanunshi daga kanta, yace "let's go" dasauri Sharif yace "check ko she's alive common Asad, are you this heartless" wani mugun kallo yama Sharif zaiyi magana wata yar tsohuwan dake cikinsu tace "bawan Allah matsamata ciki in ruwa tafito tanada rai idan baifi to ba ba rai" kaman bazaiyi ba saikuma ya matsa inda take kwance dasauri Uwani ta matsa hannunta ya kalla saikuma yakai hannunshi yakama hannunta yana duba pulse dinta bai sami pulse a hannun ba sai uban sanyi da hannunta yayi kaman kan kara, hakan yasa ya ijiye hannun yakai yatsunshi biyu kan jijiyan dake gefen wuya anan yasami wani very very weak pulse dasauri yazare hannunshi yace "she's alive" "Alhamdulillahi Rabbil Alameen" yan gidan suka fadi hannayenshi biyu yasa akan cikinta yashiga matse mata cikin da karfi yana kallon fuskanta sai chan ya tsaya yakalli Uwani dake gefensu tana kukan murna ganin tana raye yace "bude bakinta kihura mata iska aciki" dasauri Uwani tazo bude bakinta tayi tahura iska ciki yace "ya isa" daina wa tayi shikuma yacigaba da matsa mata cikin, ruwan gashinshi nabin fuskanshi har zuwa hanci, amman shiru saida yasa Uwani tahura mata iska harsau uku amman shiru hakan yasa Sharif yace "common kai kasan komk nakan harkan ruwa, ka asalin this thing ba kahura mata iskan dakanka mana, let's help the poor girl" ko kallon Sharif baiyiba yakalli Uwani yace "sake huramata" dasauri tsohuwan tace "bawan Allah kayakuri dan Allah kataimaka mata tafarfado hankalinmu duk ya kwanta inda mahaifiyar ta na nan datakusan mutuwa dan Allah kataimakama marainiyan yarinyar nan da iyayenta basu anan" kaman ya kurma ihu yakeji amman yadai daure da kyar dan matsowa wajen kanta yayi yana kallon pink lips da dan karamin bakinta dazai daura nashi akai, kaman wanda ke tsoro yakai bakinshi gently yana kallon fuskanta yadaura kan nata ko mugun sanyin da jikinta yayine yake shiga nashi oho jiyayi jikinshi yadauki wani mugun sanyi daurewa yayi ahankali yahuramata iskan bakinshi zuwa cikin nata kaman wani magic tarrrr yaga tabude idanunta dasukai wani masifan haske sai cikin nashi suna kallon juna saikuma wani uban tari datayi white tana kallonshi duka ruwan daya taho daga bakinta sai nashi dawani irin mugun sauri yacire bakinshi daga nata yaciro kanshi yajuya yana wani irin kakarin amai babuma wanda ya lurada shi sai wani irin ihu da hamdala da duka mutane keyi na ta farfado tana uban aman ruwa aka zagayeta, ganin yakasa aman yasa ya yunkura zai tashi jiyayi an kama hannunshi gam dasauri yajuyo yakalli hannunshi gani yayi Du'a dake amai sosai tarike hannunshi gam tana kallonshi har lokacin da idanun nan nata da kaman bata hayyacinta, dasauri yajanye idanunshi dagakan hannun yakalli fuskanta idanunta kadan suka budu amman shi take kallo saikuma jikinta yafara bari tana kakkarwa, fizge hannunshi yayi daga nata dasauri yana yarfewa danjjn hannun yayi kaman ya sandare yakalli Uwani dake kanta yace "ku chanza mata kaya ku rufeta shes cold a kaita asibiti" sanan yawuce wanshi batare daya kalli Sharif ba yace "wlh nakai mota baka zona saidai kadawo gida da kafa" dawani irin gudu Sharif yatashi yabishi abaya yana kara waigen Du'a da aka zagaye, mota suka shiga Sharif yaja motan da gudu. Agaban wani gida mai kama da mansion sukai horn bude musu akayi suka shiga, Sharif na parking yabude mota yafito yana attishawa, daidai wata kyakkyawan mata tana sanye dawani hadadden lace tafito kana ganinta kaga mamanshi sabida kamanninsu tana ganin dan nata ta tsaya turus tana kallonshi ganin yanda yay sharkap daidai nan shima Sharif yafito yana murmushi dasauri takaraso wajen tace "what on earth happen daka jike haka son" ranshi abace yace "lemme shower Ammi" yay wucewan shi, tabishi da kallo saikuma tajuyo takalli Sharif dataga yana murmushi tace "maiya faru yaji ke haka Sharif kaima jibi yanda kai daka daka kaman kai wasa a mud"? Dan dariya yayi yace "aikin Allah mukayi Ammi" aikin Allah? ta maimaita gyadamata kai yayi yace "Ammi we just saved a girl dabadan muba data mutu arijiya wlh, Asad yacirota daga rijiyan nikuma na ciro both Asad and the girl, nima bari naje nai wanka" shima yawuce yabar Ammi awajen baki bude. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR free page EPISODE 🔟 Gban wani hadadden flat yayi ya bude kofa ahankali yashiga, kaga flat din zaka dauka a turai kake, sama yayi yabude wani daki da komi nacike kenan blue, bathroom yabude yashiga danyay wanka, koda yafito shiryawa yayi cikin 3 quarter da singlet fara, sanan yafito anan falon sama yaga Asad zaune dagashi sai towel daya daura a waist dinshi fari, tulin gashin kanshi ajike da ruwa yana tsiyayar da ruwa, ruwan nabin fuskanshi yana diddiga akan kirjinshi gwanin ban sha'awa, dark skin dinshi nawani irin glowing dankomai bai shafaba yana fitowa daga wanka yatuna da abinda yakeyi dazu a mota yazo yazauna yacigaba, kirjinshi kaman zai fashe acike tsabagen work out gashi da uban hair akirjin dasuka kwanta sukai lub lub har wajen cibiyanshi da maranshi, hakama muscle dinshi amurtuke yadaura MacBook din akan cinya nashi yana danne danne ya mikarda kafafun shi yadaura kan wata cushion. "katashi kasa kaya Asad yanzun nan fa kabar cikin rijiya kayi wanka basaikasa kayaba" kaman ba dashi ake magana ba yamai banza dan haushin shi yakeji sabida abinda yamai dazu, tabe baki Sharif yayi yace "koba komi dai after such a long time nasa kayi taimako u just save a life today wired dude kawai" dago kanshi yayi yawani kalli Sharif din irin kallon nan na dani kake, dagamai gira daya Sharif yayi sanan yawuce yace "am starving idan kagama come down muje ka gaida Dadda, nidai natafi wajen Ammi naci abinci" yawuce yasauka kasa abinshi batare daya karabi tanan Asad dinba tunda yaga fitina yakeji, baitaba ganin fitinannen yaro dan bala'i irin Asad ba. Yadade yana danne danne sannan yarufe system din yatashi daidai lokacin iPhone 13pro max dinshi tahau ringing kobai kalli screen dinba yasan Ammi ce hakan yasa yadauki wayan yakara a kunne cikin muryanshi dakeda dan sanyi yace "Ammi gani nan zuwa" katse wayan yayi ya jefar kan kujera sanan yashiga wani daki, shi dakin komi off white ne ba kaman na Sharif ba, hoton dake jikin bango nashi zaisa kagane wanan dakinshine, gaban madubi ya tsaya dayacika da kayan shafa sanan yadau cream ya shafe jikinshi kafin yabude wardrobe yadauko wani 3quater maroon da white t-shirt yasaka dasukamai kyau sosai sanan yakoma gaban madubi wani man gashi yabude sanan yalukata yashafa akanshi kafin kaceme gashin su kara wani kanannadewa bakinsu na shinning kaman wani gashin jariri sanan yadau turarukanshi ya feffesa yadau yazura wani crock na maza yafito falon saman, wayanshi yadauka sanan yawuce yafice daga flat din, yana fita wani rana yadaki fuskanshi tsaki yayi yace "I hate this damn country" Babban flat din gidan yayi kofa yabude ahankali yashiga Sharif ne ke zaune afalo sai wasu yan mata guda uku Aneesa, Rahima, da Mariya duk suna zaune kusada Sharif din suna hira, suna ganinshi tsit kakeji wani irin batarai yayi kaman baitaba murmushi tunda yazo duniya yazo zai wuce tagaban su dasauri suka shiga gaidashi. "Ya Asad welcome ya hanya" da kyar ya iya bude baki ya amsa batare daya kallesu ba. "fine" that's the only thing yafadi sanan yay dinning Sharif nabinshi da kallo saikuma ya kalli Aneesa data bishi da kallo kaman zata hadiyeshi. Zama yayi kan kujera daidai lokacin Ammi tafito daga kitchen rikeda flask tana kallon fuskanshi tace "sannu da aiki superman mai shiga rijiya, yanzun nan nagama hadamaka tea dinan zokasha koya kori sanyin daya shiga jikinka" dan murmushi yamata daidai tamikomai cup din shayin dayaji kayan kamshi karba yayi itakuma taja kujera kusadashi tace "Ya hanya" ahankali yace "Ammi yaushe zamu koma gidanmu"? "to marason zumunci anan kano zaku cigaba da zama" dasauri yadago kanshi wata hadaddiyar mata ce kyakkyawan gaske tana sanye da bakin jallabiya kesaukowa, ahankali yace "ina yini Anty" hararan shi tayi sosai tace "kai yaron nan ina kanwar mahaifinka kana kirana da Anty, abinda kike koyamai kenan Maryama? Kaf family nan bamuda yaro mara tarbiya irin Asad" sanin halinta yasa Ammi tace "stand up and greet her properly Asad" kallon Ammi yayi yanda ta gyadamai idanu yasa yatashi ahankali yana kallon kasa yace "ina yini M...um" washebaki tayi takaraso inda yake hannunta takai kan fuskanshi tace "ko kaifa Asad, kadawo lpy" kanshi akasa yace "lpy" murmushi tayi tace "ance kadawo kayi aikin nanne na youth start up forum ko da government sukai establishing right?" gyadamata kai yayi batare daya kalleta ba, cikeda gamsuwa tace "awani tasha zakuyi Channels television news" murya chan kasa yace "kowani TV station zasusa har nagama na 7days" gyadamai kai tayi tace "Masha Allah, Allah yataimaka, saikuma batun aure ko" shiru yayi sakinshi tayi tace "anyway nadawo mayi maganan da kyau, let's go girls" tashi matan sukayi suka bita suka fice. Daure fuska yayi sosai yanajan cup din tea dinshi zaikai baki yace "saisa banason zuwa gidan nan I don't like her Ammi, this Anty Turai" shareshi Ammi tayi tajuya takalli Sharif dakecin abincin shi tace "you want more Sharif" "Ammi am full" kallon Asad din tayi tace "mezakaci"? kallon abincin data bubbudemai yayi sanan idanunshi suka sauka kan spaghetti da meat balls da hannu yanuna mata zubamai tayi ya karba yashiga ci ahankali bin dan nata take da kallo take, anytime taganshi mahaifinshi kawai take gani halinshi sak dana ubanshi, juyowa tayi takalli Sharif tace "baku bani labarin ciro yarinyar dakukayi daga rijiya ba" kaman jira Sharif yake yace " Ammi I was driving fa kawai wata mata tasha gabanmu tana kuka wai mutaimaketa yarinya tafada rijiya, Ammi I was begging Asad fa yaje mucirota wai bazaiyiba gashi ba maza sai tulin uban mata kaman gidan biki duk suna kuka, shine nace musu mujeni nacirota dan nasan that's the only thing dazai fitoda Asad daga cikin motan nan danni kadai nasan irin mugun halinshi, aiko ina shiga saigashi yataho ashedai yana sona yasan ban iya ruwaba fear of my death yasa yazo bawaidan he meant to save the girl ba, shine yashiga fa yacirota, Ammi kinsan menene" yay maganan yanajan kujera da sauri yana zama sanan yakalli Ammi dake kallonshi yace "Ammi nifa dasuketa yarinya I thought small girl ce fa tafada rijiyan saigashi Asad yafito da zankadediyan budurwa innalillahi Ammi kinga kyanta kuwa" Ammi dake sauraronshi tace "haba" dasauri yakalli Asad dake cin abincin anatse yana danna waya yace "Asad isn't the girl beautiful" batare daya kallesu ba yace "I don't know bankalleta ba" wani mugun tsaki yaja yace "Ammi wlh Asad dan rainin wayau ne" dan dariya Ammi tayi ganin yanda Sharif ya tunzura sosai tace "don't mind him kaji cigaba da bani labarin" murmushi yama Ammi yace "wlh Ammi tunda nake Allah Ammi harna gama yawona across the globe ni bantaba ganin kyakkyawa irin yarinyar nanba Ammi she don't even look Nigerian, hala half cast ce, Ammi she's so pretty gashinta har waist, she's so pretty I wish I can even see her again" ture plate din abincin dayagama ci Asad yayi yamike Ammi dasauri ta kalleshi tace "harka koshi? Baka cinye ba ai" gyadamata kai yayi yace "ya isheni, natafi wajen Dadda" dasauri Sharif yatashi yace "wait for me Asad" ko kallonshi baiyiba yawuce Ammi tabisu da kallo tana murmushi, Sharif is such a gentle man with a very very forgiven spirit, shikuma Asad is opposite na hakan, churarren mutum ne baka gane gabanshi da bayanshi ko itama sabida ita tahaifeshi ne saisa take iya fahimtan halinshi tass,. Wani flat suka shiga kayataccen falo ne da kujera ke ciki sai lallausan carpet da aka rufe ko ina na kasan dakin dashi sabida sanyi sai wani tsohon dattijo da akalla zaikai shekara 90 ko fin haka ke zaune kan wata kujera mai ultra taushi wacce kanagani kasan musamman sabida shi akayita yana zaune gashinan tsaf tsaf sai wani bakin glasses a idanunshi hannunshi rikeda ayaba yanaci da aka yayyankamai awani clean bowl, tunda yashigo gidan this is the first time yayi kayataccen murmushi yace "Dadda" da sauri tsohon dake tauna ayaba abaki ya tsaya chak saikuma da sauri yasake gyara zaman glass dinshi a idanunshi yakalli kofa sabida haske kofa yasa baiganesu ba cikin muryanshi ta tsufa da still kuma take fitada kyau yace "amaida kofan arufe" dasauri Sharif dake hadiye dariyan shi yamaida kofan yarufe hakan yabashi daman ganinsu ahankali yanuna Asad da yatsa yace "Sharif Asad nake gani" dawani irin sauri Asad yaje bowl din jikinshi yacire ya ijiye agefe sanan yawani rungume kakanshi tsam tsam yace "Dadda kai kadai nayi missing wlh, kaga Sharif tunda na shigo garin nan yake batamin rai Dadda" washe bakinshi da hakora sun fiffita yayi yace "to wlh su kiyayeni aina gayamusu duk wanda yataba Asad toni yataba kona mutu bazan yafemai ba" dariya sukayi duka Sharif yazo yace "Dadda kai bazakamai fadaba mugun halinshi yay yawa" hannu yamika ya kamo hannun Sharif yace "banace ku hada kanku ba kome yayi kamai hakuri, shi hali zanen dutse ne ko mutum zai rabu dashi saidai da kadan kadan, halin mahaifinshi Abdullahi yagado sak" kankameshi sosai Asad yayi yace "i love you Dadda na" 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR wa.me/+2347012181461 Free page EPISODE 1️⃣1️⃣ Da taimakon Matan dake compound din aka kwasheta akai falonsu da ita jikinta na mugun barin sanyi daidai lokacin motarsu Abba tai parking akofar gida wani irin azababben gudu sukayi dayake Hamad shiya tukasu da Mami da Abba ne kadai sauran duk sun barsu awajen Kaka achan Ikara, dawani irin gudu Mami tashigo gidan idanunta sunyi jajir, this is the first time data iya cire koma meke sata yima yarta wani kala tanuna tsantsan damuwa da so akan yartata tadubi matan tace "ancirota ancirota daga rijiyan? jama'a kufadamin ina y'ata Du'a, ina take"? Tai maganan tana kama kirjinta dataji yana wani irin bugawa tsabagen fargaba, daki matan gidan suka nunamata sukace "tana daki, yanzun nan aka shiga da ita ciki" dawani irin gudu Mami tai flat dinsu Abba ma dayashigo yabita dasauri Hamad shima dagudu yabisu da shine last na shigowa sabida parking mota dayake, tana shiga falo taga some few mata akan Du'a dahar lokacin take ajike akasa tana wani irin rawan sanyi hakoranta na karkar kar kaman ana hada kacha ana gwarasu, wani irin ihu Mami tayi. "Du'a! Du'a" yanda Mami tayi baya kaman zata sume yasa dasauri Abba yatareta yace "calm down" juyawa Matan dakin sukayi suka fice ganin maigida, daidai Uwani tasauko kasa dawasu kaya da bargo daban daban a hannunta, tashi tayi daga jikin Abba dasauri takarasa wajen Uwani, karban kayan hannunta tayi sanan takoma inda take, dagota tayi dasauri takalli Hamad tace "Hamad bani wuka" dagudu yay kitchen wuka yadauko yafito yaga rigan jikinta Mami tayi Abba da Hamad duk suka juyar dakai chanza mata kayan Mami tayi agurguje sanan tawani irin rungume yarinyar dasauri tarufeta da bargo tana kuka. "I am sorry Du'a sorry" matsowa wajen Abba yayi hannunshi yakai yadaura kan wuyanta jin sanyi yasa yakalli Uwani yace "jeki hado garwashi" sanan yaciro hannun Du'a daya yana murza tafi hannun dasauri Hamad shima yazo yakama dayan hannunta yana murzawa duk tana jikin Mami data kankameta sosai, ba'a wani dauki lokaci ba saiga Uwani da uban rushi a kasko dan makota taje tasamo, ajiye wa sukai agabanta still suna murza hannunta ahaka suka samu kadan kadan tarage rawan sanyin hartazo tada ina gabaki daya kallon fuskanta tayi yanda idanunta ke a lumshe shafa fuskanta Mami tayi ahankali takira sunanta. "Du'a" bude idanunta kadan tayi saikuma tabudesu gabaki daya tana kallon fuskan Mami, dasauri Hamad yataso kansu yana kallonta yace "Du'a taya kika fada rijiya"?zubamishi idanu tayi shima tana kallonshi saikuma ahankali tamaida idanun kan Mami tana kallonta asanyaye, Mami hakanan taji jikinta yay sanyi sabida yanda yarinyar ke kallonta, hawaye taga sun zulalo ta gefen idanunta kafin ahankali tabude bakinta cikin muryanta dabata fita sosai tace "maisa aka cironi daga rijiyan eh? Mami inaso namutu kowa yahuta saisa kodana fada saidai nadinga lumawa cikin ruwan ko tsoro daya banji ba saima kwanciyan hankali danaji domin ajalina yazo, Mami naso namutu sabida kihuta hankalinki ya kwanta kince tundaga randa kika haifeni baki karasamin kwanciyan hankali ba, yau dana fada rijiya all I could thought of was yanzu zaki fara samin kwanciyan hankali, bazan kara jawo matsala agidan nanba, bazan kara saki ko Abba a matsalan Kaka ba, Ya Nana zata auri Muhsin dinta, bazan kara zamema kowa matsala ba, Abba bazai kara wahalan boyeni ba dan nariga namutu" yanda take maganan tana kuka mara sauti sai hawaye kobakada imani sai zuciyanka ta sosu, ahankali tace "Mami akwai wata tambaya dana dade inaso namuku keda Abba" taidan shiru saikuma ahankali tace "bayan kun haifeni maisa tun a asibiti dakuka ganni daban bakusan yanda kukai dani ba maybe ko kuce baku sona a kaini gidan marayu kokuma kuce a chanza muku yarinya bani kuka haifa ba, maisa kuka daukeni still kuka raineni maisa kukamin haka, wanan kalan rayuwan dakukasa inayi kullum zaban mutuwa nakeyi akanta dan tafimin alkhairi I just want to die nahuta, dan Allah kubarni na mutu" tafashe da kuka sosai dayasa daga Abba Mami da Hamad were damn speechless itako Uwani dake gefe kuka tadingayi, tadade tana kuka ajikin Mami babu wanda yay attempting hanata ahaka bacci yay awon gaba da ita, ahankali suka kwantar da ita akan kujera suka lullubeta sanan Mami tazauna gaban kujeran tana kallon fuskanta, Tashi Hamad yayi yakalli Abba da Mami yace "Abba I want to see you both" yay sama tashi Mami tayo takalli Uwani da jajayen idanunta tace "ki zauna da ita" gyadamata kai Uwani tayi Mami tawuce sama itama, Abba yadade tsaye awajen sanan yawuce yay sama, dakinshi Hamad yabude ya shiga Mami tashigo Abba dashine na karshe shima yashigo yasami waje yazauna, kallon Abba Hamad yayi yace "Abba what are you going to do? Yaya zakayi da maganan Kaka?" kallon Hamad yayi yama kasa magana saikuma chan yace "all I know is bazan taba iya koran y'ata daga gidan nan ba" dasauri Hamad yace "Abba yazakayi da bakin Kaka, tace inhar yarinyar nan batabar gidan nan ba bata yafemaka ba, itaba mahaifiyarka bace kaza kaza kaza, Abba Kaka ta tsufa and we all know yanda tsofaffi sukai believing akan all this superstition, Du'a tazaman ma gidan nan da family mu gabaki daya matsala, jibi duka su Baffa dazu sunce duk akoreta ni I think inhar hakane zan dauki Du'a natafi da ita chan Jaji tai zamanta a apartment dina" dasauri Mami tace "Hamad duk randa mahaifiyar ka tasan kaika tafi da Du’a abin bazai muku kyau ba, kuma Du'a mace ce bazaiyi kyau tayi rayuwa dakai kai kadaiba dama kanada mata ne, ni kaina ayanzu all I want is peace, tunda Du'a ce matsalan afitarda ita daga gidan saisa na yanke shawaran kaita wajen Mama na achan Abuja" kallon Abba tayi ahankali tace "Dadyn Hamad" kallonta yayi yay shiru batare dayace komiba, ahankali tazo kusadashi zama tayi sanan takama hannunshi tarike tace "I know tunanin dakake da abinda ke ranka, mu dinan bamuke kula da Du'a ba wlh Allah ne, so it's high time we free this girl mu mikama Allah komi and I assure u idan tana hannun Mama she's safe nasan Mama na, I don't want u to be stubborn, u are a family man, ba Du'a ce kadai yarka ba, sauran ma dole ka kalli yanda rayuwan su zata cigaba da gudana, sabida Du'a kar peace da family ka ya wargaje just look at what Nana is going through now itama ai yarka ce, the way u look out for Du'a itama haka kake looking out for her, kayakuri kaduba lamarin kaji" tunda take maganan yake kallonta harta gama, ajiyan zuciya yasauke sanan yace "I will think about it, kubani waje yanzu" gyadamai kai kawai Mami tayi ta tashi tawuce tafice, yakalli Hamad yace "ka kira Dr na yazo yadubata tashi katafi" tashi yayi ahankali yafice shikuma Abba ya kishin gida da kujera ya lumshe idanu Allah kadai yasan meke going azuciyanshi. Wuraren magrib likita abokin Abba wanda shine likitanta tun tana yar karama yazo yadubata allura yamata sanan yabata magunguna Abba ya sallameshi yatafi. "she's alive! she's alive I can feel her pulse" sama sama takejin maganganun nan kaman a eco saikuma chan tabude idanunta sukai clocking da nashi......tarrrr tabude idanunta daga baccin datake tanabin inda take da ko'ina na dakin da kallo, ganin tana dakinsu kan gadonta ne an lullubeta da bargo, mafarki take kenan, mutumin data bude ido tagani dazu yacirota daga cikin rijiya tagani yanzun nan amafarki, ahankali ta yunkura ta tashi zaune ta jingina da bango tana kallon ko'ina ganin gari yama soma wayewa, saukowa tayi daga gado sai alokacin taga wani jibgegiyan akwati da batasan daga ina yazo ba baka kwara daya atsaye gaban wardrobe dinsu, bathroom dinsu tawuce tashiga wanka tayi da ruwan zafi sosai tana karajin karfi ajikinta sanan tafito daga wankan daidai lokacin Mami nabude kofan dakinsu tana shigowa hada ido sukayi da Mami ahankali ta sunnarda kanta kasa tana tuna all maganganun data gayama Mami jiya suna dawomata fresh a memory dinta kasa motsi tayi itama Mami tadauke kai tawuce wardrobe wasu kaya taciro mata tajuyo ta ijiyesu kan gado tace "ki shirya kiyi salla bari naje nakawo miki breakfast". Fita Mami tayi daga dakin itakuma tashiga shiryawa agurguje sanan tahau kan dadduma tai salollin dake kanta saida tai azkar sanan ta tashi ta cire hijabin tazauna akan gado, bude kofa Mami tayi tashigo dauke da tray na abinci sanan takaraso cikin dakin ajiye abincin tayi kan side drawer gadonsu sanan tadawo tazauna ahankali kan gadon kusada Du'a da kanta ke kasa har lokacin dan wani irin kunyan Mami taji tanaji, murya chan kasa tace "Mami ina kwana" shiru Mami tayi tana kallonta batare data amsa ba saikuma gently takai hannunta kan fuskarta ta tallabo habarta hakan yasa tadago idanunta ahankali takalli Mami, murya chan kasa Mami tace "Du'a" ahankali tace "Mami I'm sorry Kinji" murmushi Mami tayi tace "shiiii I want you to listen to me" gyadama Mami kai tayi, Mami tadan numfasa tace "all abubuwan dakikaga nida mahaifinki namiki badan mun tsaneki bane saidan we are all trying to protect you Du'a, Du'a nasan kinsan wanan abin dan nasan kinsha jin yan uwan Abban ku nafadi, dana haifoki babu kalan maganan da ba'a fadiba akanki, ance ke ba yar Abba bace, naje na nemi ubanki nahadaki dashi, ke mayya ce ke yar ruwace" shiru Mami tayi tana sauke ijiyan zuciya sanan tace "Du'a akwai many things which u don't know kuma banmason kisani, I fought mahaifinki, we fought hard muka samu yan uwanshi da Maman shi suka barki kika zauna agidan nan left to them koranki sukaso ayi" Mami tasakeyin shiru sanan ahankali takai hannunta tadaura kan kumatun Du'a dake kallonta ahankali tace "Du'a you are special! tun ranan damuka haifeki mukasan hakan, you are special saisa kikaga muna boyeki, Du'a ke dabance! muna boyeki ne cus munyi tunani ta hakan zamu iya kareki and protect you, but u got it all wrong kin zaci mun tsaneki ne amman bamu tsaneki ba, kintuna abinda yafaru dake a JSS2 dayasa Abba yahanaki fita at all kinaso yakara faruwa dakene" girgixa ma Mami kai tayi dasauri hawaye nacika mata idanu. Ahankali Mami tasauke ijiyan zuciya tace "nakira Mama, Grandma dinki tariga tasan komi dama, yanzu da safen nan Hamad zai kaiki chan wurin ta a Abuja harsai komi nagidan nan ya daidaita, I think kema is best for u, your childhood has been terrible, kin taso cikin kyaran kowa is high time kije inda nasan u will receive d best care batare da an kyareki ko an ware ki ba, kinason kije wajen Mama na ko" ahankali ta gyadama Mami kai hawaye na zubomata, hannu Mami takai tashare mata hawayen tace "nasan namiki laifi, I've wronged you in so many ways just to please yan gidan nan but bazan karaba, nina daukeki na raineki for 9 months I can never hate you, abinda nakeso dake is take very good care of yourself, kizama yarinya mai wayau da basira, know when u are in danger and when u are not, kidage da addu'a, ki rike Allah danshi kadai ya isarmiki, I want you to be a good girl, karki sake kima grandma dinki ko any of your uncles rashin kunya kinji Du'a, I know u are in a good hands this is the first time dazaakije wani wuri da hankalina ya mugun natsu, now eat your food saiki fito ki gaida Abban ki kuyi sallama bari nakai jakan I waje" gyadama Mami kai tayi Mami ta tashi jakan taja tawuce tafita daga dakin, shiru Du'a tayi Allah ma yasan har cikin ranta tana farin ciki zatabar gidan nan sabida tasan yanda Maman Mami kesonta lokacin tana yarinya idan sukaje gidan kaman zata cinyeta, koba komi bazata kara ganin Muhsin ba, mugun mutum, koba komi idan baiganta ba zai hakura ya auri ya Nana, Hawwa zata huta da hararanta kullum Mum ma tahuta babu wanda zai kara kiranta yar aljanu, and at the same time yau saitaji wanan bakin cikin da kunci na haushin Mami dayakeji dukya fita daga zuciyanta sabida fir the first time Mami ta zaunar da ita tamata bayanin abinda bata taba mataba kenan. hannu tamika tadauki tray abincin ta abincin taci bama tawani ci sosai ba ta ture ta ijiye, shigowa dakin Mami tayi takalleta tace "tasoto muje kiyi sallama da mahaifinki" gyadama Mami kai tayi gabanta nafaduwa hijabinta tasaka sanan tabi bayan Mami suka fito, Abba na zaune akasa yana karanta jarida hangita yasa ya tsayar da karatun yana kallonta harta karaso, dan nesada shi ta tsugunna ahankali tace "ina kwana Abba" "ya jikinki akwai abinda ke miki ciwo"? Abba yamata tambayan bayabo ba fallasa wanda idan tasabo tasaba dan Abba naturally he's not that kind of a friendly father dake wasa da yaranshi, gyadamai kai tayi ahankali tace "babu ko'ina Abba" gyadakai yayi cikeda gamsuwa yana kallonta, batare data dagokai ba tace "Abba kayakuri bazan kara abinda nayiba" ahankali yace "l know" dagokai tayi ta kalleshi, hannu yasa a aljihu yaciro bandir nayan 200 20k yace "zo" tashi tayi ahankali takarasa gabanshi karba tayi ahankali tace "nagode Abba" "Allah kiyaye hanya, jeki Hamad na jiranki a mota ta" hakanan batasan mesaba kawai taji kuka yazo mata dasauri tajuya tana daura hijabinta kan fuska Abba kuma yabita da kallo, fita tayi daga falon, Mami ta biyota abaya rikeda hadadden kula na abinci. Hamad na tsaye gaban motan sienna Abba yaga fitowanta yana kuka, murmushi yayi yabude mata gaban motan tana karasowa tashiga ta zauna, karasowa itama Mami tayi tana murmushi tace "bazakama kanwarka magana tarage kuka ba tadauka yarinya ce ita" murmushi yama Mami baice komiba, Mami ta ijiye mata kulan akan cinyanta tace "ga abinci inkinji yunwa kici naga baki waniyi break da kyau ba and stop crying" gyadama Mami kai tayi, tashi tayi takalli Hamad tace "kutafi Allah kiyaye hanya" rufe kofan yayi sanan yazagaya yashiga yatada motan yaja Mami namusu bye bye suka fice daga Gate din. ajiyan zuciya Mami tasauke ahankali tace "Allah ya azurtaki da farin cikin rayuwa Du'a, I love you so much y'ata, zan dinga miki addu'a kinji Du'a" 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR Free page EPISODE 1️⃣ 2️⃣ Sosai Hamad ke zuba gudu akan titi, har cikin ranshi he is happy for Du'a na barin gidansu datayi, bini bini yake kallonta yanda saibin hanya da komi take da kallo kana gani kasan bata saba fitowa ba, dan juyowa yayi yakalleta ganin yanda take kalle kalle yasa yay dan murmushi yace "iyye basaban ba yau anfito waje" juyoda kanta tayi takalleshi washemai baki tayi tana murmushin nan mai tafiyar da imanin mutum tace "Ya Hamad rabon dana fito waje wlh harna manta nafi shekaru" murmushi yamata yace "this is a chance da Allah yabaki, remember abinda nafada miki duk wanda yadogara ga Allah to Allah ya isar masa, cikin sauki tashi daya Allah yacireki daga kuncin gidan mu, so babu abinda yagagari Allah muddin ki kayi imani, just always thank Allah kinji and be a good girl" gyadamaikai tayi kaman mai tunani tace "Ya Hamad nifa nama manta kamannin Maman Mami fa Grandma, tun ina karama da Mami ta taba zuwa dani ban kara zuwa ba, saidai muyi magana awaya, su Aneela ne suka santa" dan murmushi yayi hankalinshi nakan hanya yace "grandma dinki is one of the nicest person I know in this world, tanada kirki gatada son mutane, duk naje Abuja sainaje na gaidata, you are so lucky to have her as grandmother" shiru Du'a tayi kaman tana tunanin maganan shi saikuma chan ta kalleshi tace "Ya Hamad maisa kai u are different agidan mu? baka biyema su Mum da Ya Nana, kafisu kirki duka" yana kallon hanya still yace "let's say sabida ni namiji ne I see life differently daga yanda mata keganin life, and Abba yabani tarbiyan da nakan iya banbance right from wrong" murmushi tayi takalli kulan kan cinyarta tashiga budewa name ne soyayye da Irish da plantain. "bani nama naci" turo baki tayi tadauko nama daya takai tasamai akan hannunshi dayake bata, murmushi yayi ya wurga abaki yana taunawa yace "wow girkin Mami always taste different" nama daya itama ta dauka tamaida kulan tarufe sanan tahauci tanamai hira kadan kadan harta cinye sai bacci, kallonta yayi ganin yanda take bacci yasa yay murmushi gabgarawa gefen hanya yayi yay parking Sana yadan taso yasaukar mata da kujeran sanan yakoma mazaunin shi yatada motan yana bata wuta. Wuraren 1 suka kai Abuja, tadata yayi ta hanyar kiran sunanta. "Du'a, Du'a" bude idanunta tayi kadan, hararanta yayi yace "duk uban baccin dakikayi jiya bai isheki ba yarinya saison bacci" tashi tayi yace "gyara kujeran" gyara kujeran tayi yataso sanan takalli hanya yace "kinga yanda Abuja keda kyau kalli titi ba irin na Kanon Kuba" murmushi tayi tace "mun kuwa kaiwa gidan" gyadamata kai yayi yace "takirani yafi sau uku duk kina bacci" shiru tayi tana kallon ko'ina kaman zata hadiye garin da idanunta saiwani irin sanyi da shauki takeji har sukakai wani estate mai suna Presidential Estate. zaro ido tayi tana kara kallon ko'ina ganin gidaje masu suna gidaje ba muna gidaje ba, tasha ji idan su Mum na gulman su tana yawan cewa ai Abba sabida ya rainata yar gidan masu kudi yaje ya auro mata, itama yarinyar kaman mayya itace kawai ta auri talaka mahaifiyarta tabarta ne sabida ita kadaice yarta mace, ita bazata iya tuna gidan dasuke zuwa a dan memory dinta na Grandma sonta lokacin tana yarinya akazo kuma aka dena zuwa da ita saidai su Aneela da Muhammad da Mudasir. Shiga Estate din yayi yana tafiya ahankali ganin yanda Du'a is enjoying the view din, agaban wani lafiyayyen gida Hamad yay horn, wani security yafito ganin Hamad yasa yace "barka da zuwa yallabai Hajiya ta sanar dani zuwanka" gyadamai mai kai Hamad yayi yana murmushi shikuma yakoma ciki yabude musu Gate din, Jan motar ciki yayi Du'a ta kwalalo idanu tace "nan ne gidan Grandma Ya Hamad" murmushi kawai yamata yana karasa parking motansu acikin jerin motocin dakenan gidan wanda babu mate din seinna su, bude motan yayi yafito sanan yamata alamu data fito gyadamai kai tayi daidai security yagama kulle gate yazo yace "akwai akwati ne Yallabai" "oh yeah" Hamad yafadi yana budemai booth daidai lokacin Du'a takaraso wajen tsayawa chak security yayi yana kallonta ganin haka yasa Hamad yace "ga akwatin" dasauri yajuyo yakalli Hamad hannu yasa yadauki akwatin yawuce Hamad kuma yarufe booth din yajuyo daidai lokacin wata hadaddiyar mata wacce kana ganinta kasan ba yarinya bace dan ta ijiye jikoki tafito, tana sanye da bubun atampa ajikinta gatanan black beauty da akalla zatakai 70. "oyoyo oyoyo, su maigida an iso" jin muryanta yasa dasauri Hamad yajuya washe baki yayi yace "Hajiya wanan kwalliya haka, bazaki barma yara ba" dakuwa tamai tace "kaci gidanku, yanzu dani dasu idan akaje gasan kyau basai akwasheni sau dari baza'a kwashe suba" karasawa yayi har inda take sanan cikeda girmamawa yadan runtsuna yace "ina yini Hajiya" hannu tasa tashafa kanshi tace "kasha hanya Soja na maigida, jekai wanka kahuta kaida komawa kano sai gobe" tai maganan tana kallon Du'a dake bayan Hamad kanta akasa tana wasa da hijabinta kunya yahanata dago kai. "Du'a" matar takirata ahankali, ahankali Du'a kaman wacce ke tsoro tadago kanta takalli kakanta fess tagane ta danga kamanninta da Mami nan, black beauty abinta yar gayu, ganin takasa magana yasa dasauri tabude mata hannu tace "zonan zoki rungumeni, taho taho" ahankali Du'a taje dasauri tashige jikinta takankameta kankameta Hajiya tayi tace "Alhamdulillah Alhamdulillah, Du'a sannu, sannu kinji, akwai abinda ke miki ciwo"?girgizamai kakan nata kai tayi, dagota Hajiya tayi tasa hannu tai cupping face nata tana kallonta kaman yanda Du'a me kallonta ahankali rasama mezatama yarinyar tayi hakan yasa ta manna mata kiss a goshi sanan takama hannunta tarike tace "muje nakaiki dakinki kiyi wanka" Ciki tashiga da Du'a falon wani irin hadadden gaske gashinan Duplex sai yan aiki guda biyu dataga suna gyara dinning suna ganin Du'a duk suka bitada kallo suna gaidata. "welcome Du'a" murmushi Hajiya tayi tace "kingan su suke tayani aikace aikacen gida, wanan sunanta Shema'u, dayan kuma sunanta Razika, duk sun sanki, jeki musu sallama" gabansu taje ahankali sai kallonta suke kaman basu taba ganin mutum ba, hannu tamika musu cikin muryanta mai dadi tace "Assalamu Alaykum, nice to meet you" dasauri suka karbi hannunta suna murmushi Razika tace "you are so beautiful" tsayawa tayi turus tana kallonsu Hajiya dake kallonsu tace "tell them thank u sunce kinada kyau" ahankali tace "thank u" sakinta sukayi itakuma Hajiya tasauke ijiyan zuciya sanan tace "taho mutafi" dasauri tajuyo kaman jira take dama stairs sukayi sukai sama saitaga ashema kasan baida kyau wani daki tabude dakin mai kyau sosai saiga hoton ta datana yarinya tana rarrafe kusada Hajiyan dasauri tashiga dakin tana kallon hoton, murmushi Hajiya tayi tace "lokacin kina yar tatsitsiya keda Mamanki kunzl ganin gida, little Du'a, jeki yi wanka kizo kici abinci zan baki labarin anjima" gyadamata kai tayi sanan tacire hijabi ahankali tawuce zuwa kofan datagani wanda ta tabbata bathroom ne saida tashiga sanan Hajiya tafita daga dakin. Saida tayi wanka sanan tafito daure da towel, akwatin ta dataga anshigo dashi tabude tadauki wata doguwan riga wanda yawanci kayanta dogayen riguna ne daidaikune riga da skirt, saka rigan tayi sky blue ce mai kyau sanan tasaka hijabi salla tayi sanan tazauna tana tunanin maganan Hajiya datace tasauko, tashi tayi ahankali tacire hijabinta ta ijiye sanan tabude kofa tafito, ahankali take sauka daga stairs tana karabin gidan da kallo, daga sama sama takejin maganan Hajiya da Hamad saikuma takarasa suna ganinta sukai shiru. "kin idar tahonan" tauna mata kusada ita akan dinning hakan yasa ta taho zama tayi wajen Hajiya tace "debi abincin ki kici" dasauri Hamad yace "kafin namanta banfada mikiba kuran nama tazo gidan nan ba" turo baki tayi Hajiya ta harareshi tace "karkaga kana maigida kanemi samin jika kuka sama zamu hau nidakai, ci abinci ki kinji kome kikeso" gyadama Hajiya kai tayi sanan tadebi rice da stew da plantain da fish tanaci, bini bini Hajiya ke kallonta hartaci rabin abincin sanan tasha ruwa haka 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR EPISODE 1️⃣3️⃣ Har dare hira suke Hajiya da Hamad, kagansu zaka dauka Hamad jikan ta ne, Hajiya wata irin mace da idan kana tareda ita you have no reason or what so ever to hate her ne, kodan sabida yaranta biyu kachal aduniya saisa takeda son mutane haka oho, danta na farko yaranshi uku dukansu Maza kuma kanana dan Mami tariga shi aure yana UK achan yake aiki sai Mami dakeda yara hudu tana aure a kano, Bayan Mami ta haifi wata tarasu, Hajiya is very very educated, lawyer ce babban gaske amman yanzu tai retire saidai she's still an advocate na Human right, batun yauba taso tadauki Du'a, akwai lokacin data kusan kulle Maman Abba wato Kaka, sabida kukan da Mami tamata ne tana rokonta yasa tahakura daga lokacin tai fushi da Mami ta shareta, saisa koda wasa bata taba taka kafarta agidan Abba ba dan batada daukan nonsense and zasuga yanda zata maida yarinyar nan, Du'a tariga tabar gidan nan kenan har abada saidai in bata raye. Ganin Du'a na gyangyadi akan kujera yasa ta tadata. "Du'a Du'a tashi kije ki kwanta adaki" ahankali ta tashi murya chan kasa tace "saida safe Grandma" murmushi tamata tace "kiyi alwala sanan kiyi addu'a kafin ki kwanta kinji" gyadamata kai tayi sanan tawuce, dakinta tabude tashiga tamaida kofan tarufe, bayi tashiga tadauro alwala kaman yanda aka umurceta sanan tafito, fadawa kan gadon tayi tana karanto addu'an bacci sanan taja bargo ta lulluba tana rufe ido fuskan mutumin nan tagani yay flashing a idanunta dasauri tabude idanunta tana yaye bargon tafito da kanta waje tanabin dakin da kallo, mutumin daya ciro ta daga rijiya she just saw fuskanshi, lumshe ido tayi ahankali still tana ganinshi saikuma ta girgixa kanta kaman tana kokarin koran abin dan bataso tana ganinshi, ahaka bacci yay awon gaba da ita...... Hajiya tashigo dakin da asuba ganin wutan dakin A kunne, karasawa gaban gadon tayi, zama tayi atabaki bakin gadon tana kallon fuskanta, Du'a is just different! ahankali takai hannunta ta kwashe gashin daya sauka a gefen fuskanta, shafa gefen fuskanta tayi tana kiranta ahankali. "Du'a, Du'a atashi daga bacci asuba tayi" bude idanunta tayi ganin kakanta yasa taji kunya murmushi tayi dasauri Hajiya tace "na tabbata yau zata yalwatu da ni'ima a gareni, wanan kayataccen murmushi dakika gaisheni dashi Du'a, Masha Allah jikata is very beautiful, barakallahu fiki, tashi kiyi alwala kizo kiyi salla kifito kuyi sallama da Hamad yashirya zai tafi" gyadamata kai tayi Sanna tasauka daga gadon ahankali bathroom tashiga itakuma Hajiya tawuce tafita. Saida tai salla sanan tafito sanye da hijabi, a falo tagansu suna zaune Hamad na rike da mug yanashan coffee, karasowa tayi ta tsugunna ahankali tace "ina kwana Grandma" "kintashi lpy Du'a ya kwanan Abuja" murmushi tayi tace "I love here Grandma, Ya Hamad good morning" "morning dama ke nake jira zantafi" yatashi bayan ya ijiye cup dinshi, Hajiya tace "sa takalmin ki kiraka yayanki" tashi tayi tasaka slippers din da Hajiya ke nuna mata sanan tabi bayan Hamad suka fita daga falon sauka suke daga matattakala kaman daga sama yace "ya akayi kika fada rijiya Du'a" dawani irin sauri takalleshi ta tsaya batare data cigaba da tafiya ba hakan yasa shima ya tsaya yana kallonta yace "answer me" murya chan kasa tace "Muhsin din Ya Nana ne yazo" dawani irin sauri cikeda mamaki yace "Muhsin"gyadamai kai tayi tabashi labarin komi iya wanda tasani, shiru yayi saikawai yay kwafa yace "muje" binshi tayi harwajen mota, sanan ya tsaya yace "be a good girl kinji, kinga yanda rayuwanki take kasancewa awajena maza so be careful kinji" gyadamai kai tayi shafa gefen fuskanta yayi yace "wuce ki koma ciki bye" waving hannu tamai tawuce shikuma yashiga mota yatada yabar gidan bayan security yabudemai gate. Ahankali da sallama tabude falonsu tashiga, Hajiya na zaune kan kujera tanacin fruits dake cikin bowl akan cinyanta, ganin Du'a ta shigo yasa tanuna mata gefenta tace "zoki zauna anan Du'a" murmushi tayi takaraso wajen tazauna, bowl din tanuna mata tace "zaki sha fruits"? gizgiza mata kai tayi tace "na koshi" murmushi tamata tace "karki damu nariga namiki friends sunje kano ne but maybe tsakanin yau ko gobe zasu dawo zaki gansu yanmata kaman ke zadan su girma miki but I'm sure u will like them" murmushi tayi tace "thank you Grandma" murmushi tamata sanan tace "yanzu abinda ke mind dina is school, banso kishiga secondary school dan kinyi girma saidai lessons, koda wasa bazakiyi rayuwan kullen nan dakikayi agidan ubanki ba, don't worry I will think of what to do akanki, yanzu dai zansa driver na yadauke ki Razika zata biki kije saloon ama gashin nan lafiyayyen gyara ko amiki kalba ko kitso duk wanda kikeso, sanan amiki gyaran farce right" gyadamai mata kai tayi tana murmushi, Murmushi itama Hajiya tayi tace "answer da naki stop nodding head be acting like a big girl okay" murmushi tayi sosai wanan karan tace "okay Grandma" "good girl, jeki shirya kiduba wardrobe dinki akwai kaya awajen kisa daga nan" harzata gyadamata kai saida sauri tace "Tom" wuce wa sama tayi Grandma tabita da kallo harta bace mata. Wardrobe din dakin tabude hadaddun karyane wanda mostly abaya ne, dogayen riguna kala kala daban daban, ahankali tadaura hannunta kan wani baki fitodashi tayi daga leda tana kallon rigan kaman Grandma ta aunata shiryawa tayi cikin rigan saikuma dagudu tai wajen madubi tana kallon kanta yanda taga tayi kyau ko Nana su bata taba ganin tasaka doguwan riga mai tsada nan ba, murmushi tayi tadaura dan kwalin saman tadauki hijabinta akai tasaka tafito tasauko kasa Hajiya na ganinta tace "ina gyalen abayan Du'a" dasauri tace "nadaura akai Grandma" dan dariya Hajiya tayi saikuma ta mike tace "zokiga" karasowa gabanta tayi Hajiya ta yaye hijabin dan kwalin ta warware sanan ta gyaramata parking gashin, takalli Razika dake wajen tace "he daukomata handbag a dakinta Razika" da sauri tai sama, taimata rolling gyalen saitai kaman wata balarabiya, saukowa Razika tayi da jaka mai kyau, Hajiya ya karba tabata tace "perfect oya kutafi to driver na waje yana jiranku" takalli Razika tace "stay by her side, saikun dawo, bye Du'a" juyowa Du'a tayi tamata waving hannu alamun bye sanan suka wuce suka fita sai murna take basabamba, mota suka shiga direban yajasu. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR Free page EPISODE 1️⃣4️⃣ Bini bini direban Hajiya dake sanye da uniform ke kallonta tamadubi, hakan yasa Razika takalleta, ganin yanda take kalle kallen hanya tana murmushin nan dake karamata wani kalan kyau nadaban yasa Razika tace "is this ur first time a Abuja Du'a?" juyowa tayi tazubama Razika mayun idanunta dakesa mutum yaji wani kwanciyan hankali harzata gyadamata kai ta tuna maganan Hajiya hakan yasa tace "eh" murmushi sosai Razika tayi tace "Abuja ai nada kyau, nima Hajiya tadaukoni daga kauyen mu takawo ni nan, sanan akwai lesson teacher dake zuwa mana karatu duk asabar da lahadi, Hajiya nason yara, kinga tunda nake a Abuja bantaba ganin yarinya mai kyau kaman keba" dan murmushi tayi saikuma tadauke kanta tamaidashi kan titi tana kallon motoci dan kunya takeji taji ance tanada kyau bamataso adinga cemata haka, ahankali tace "thank you" "yauwa munkawo" Razika tafadi ganin driver yay kwana yashiga wani babban Plaza, parking yayi hakan yasa Razika tace "sauka muje" bude kofa tayi ahankali tafito tana kallon wajen yanda akwai mutane kowa na shiga da fita abinshi, ko yanda takebin mutanen datake gani da kallo ne yasa taga suna kallonta itama oho dasauri tarike hannun Razika gam data fito tace "muje" tana rikeda hannun Razika suka wuce suka shiga wani hadadden saloon dake nan first floor, ma'aikatan suka taso suna gaidasu kafin Razika tamusu bayanin me za'amata nan aka shiga yi mata gyaran gashin. "inje insiyomana ice cream a wanchan shagon Du'a" ta tambayi Du'a da ake wankema gashi, murya chan kasa tace "eh" tashi Razika tayi tafice daga saloon din daidai angama wanke ma Du'a tulin gashin aka nannade mata gashin da towel matar tace "tashi muje dryer" tashi tsaye tayi tawuce taje tazauna ana sliding kofan saloon din aka shigo, juyowa tayida sauri tazaci Razika ce, wani Alhaji tagani yaci babban riga milk na shadda dake kyalli da akalla zaikai 60yrs baki dashi mai kyau ga gemu kadan tareda wata mata kana ganinta kaga yar duniya ga hujin hanci akan hancinta guda uku tana rikeda jaka tana taunan cingum tana sanye dawasu kaya dabasu da maraba da babu ajikinta, suna shigowa masu aikin suka taresu. "welcome Alhaji, welcome Hajiya" gyadamusu kai yayi yanabin matan saloon din da kallo one by one, zama matar dake taredashi tayi kan kujera tawani kamo hannunshi ganin ba ita yake kalloba da sauri yajuyo yakalleta jinta kamamai hannu, kashemaai idanu tayi tace "Baby kagaya musu style din da za'a min" washe baki yayi yace "kai wlh mata kun iya rigima yanzu style ne sai an tambayani, ninasan kan style ne" kallon yar aikin dake gabansu yayi wacce ke jiran bayanin su kafin sufara aiki yadan lashe baki sanan yace "okay bari muga" juyawa yayi yacigaba da kallon yan shagon, Du'a yanuna da akema rolling gashinta a roller za'a sata a dryer yace "how about that fine baby style, Zinariya kinason style din"? yamata tambayan still yana kallon Du'a da akema gyaran gashi wacce ko kallonsu ma batayiba madubi take kallo tana kallon abinda ake mata akai wanda is new to her tabama kofa baya, ganin inda yake kallo yasa Zinariya tace "katafi meeting din dakake dashi Sweet, idan kagama saika biyo kadaukeni" tai maganan tana shafamai hannunshi still datake rikedashi, dan juyowa yayi yakalleta kaman wanda ya manta da abinda ke gabanshi yace "ohh meeting dinan, to,to bari inje, saina dawo" yay maganan yana juyawa bude kofan yayi harzai fita saikuma yadawo dasauri yawuce wajen kujeran Du'a ya tsaya tagaban wajen yana facing nata directly yakare madubin datake kallo yana murmushi yana kallonta kaman yanda takedan kallonshi atsorace yace "nace nawane kudin gyaran kan Zinariya"? Ya tambayi mai gyaran kan Du'a yana kallon Du'a kaman wani tsohon maye wanda baitaba ganin mace ba sai akan Du'a, Mai gyaran gashin Du'a dake kallonshi ne itama cikeda girmamawa tace "all payments are done to Christy Alhaji gatachan the cashier" tanunamai wacce ketare da Zinariyan shi data daure fuska tana kallonshi, yana kallon Du'a still yace "in that case ba matsala, by the way young lady ur hair is beautiful" yama Du'a magana yana wani kalan kallonta, sai alokacin Du'a tadago kanta ta kallai da kyau wanan sa''an Abban tabe hakan yasa tamai shiru, wani irin hadiye yawu yayi yana lashe baki murya chan kasa yace "bala'i Allah yayi mace anan" rasa yanda zaiyi yasa yawuce yawayance yana kallon Zinariya yace "natafi Baby" yawuce yafita ya shiga hadaddiyar jeep din da aka kawosu ciki daidai lokacin Razika na shigowa rikeda ice cream guda biyu tazo inda Du'a take tamika mata tace "gashi" hannu tasa takarba tana murmushi tace "thank u" gajeren tsaki Zinariya tasaki tadauke idanunta dagakan Du'a kishi nawani irin turnuketa kaman taje tashake yarinyar takeji tadai daure dantafi karfin karaman yarinya haka. ********* Kano! Tundaga nesa yake hango yanayin Ammin shi dake tsaye achan baya, jiyayi ranshi yabaci sosai, ahankali yakalli Sharif dake tsaye gaban kantar Max Airline yace "collect the ticket" sanan yawuce yana tafiya daidai kaman dan Sarki, yau yana sanye da native kaya dasukamai kyau ba kadan ba, farin yadi yasaka anmai dinki jumper daya zauna ajikinshi chass, kafanshi yasa wani takalmin Dior mai kyau black dakeda igiya, gashin kanshi dinan as usual looking so coily and black, idanunshi yasaka bakin shade dan baison kallo sosai sai kamshi yake zubawa, wucesu Aneesa yayi batare daya kallesu ba yakarasa inda Ammi ke tsaye tana daddanna wayanta tasanya wani hadadden abaya mai tsadan gaske, dayake tabashi baya ko kadan bataji zuwan shi ba dan hankalinta ma yayi nisa dan tunani take, zuba hannunshi yayi a aljihun wandonshi yana kallon screen din wayanta dan yafita tsawo ganin number datake kira da akai saving da Maigidana yasa murya chan kasa yace "Ammi" firgigit tadan waigo ta kalleshi saukar da wayan tayi dasauri gudun kar yaga number datake kira tace "is it time for boarding already son" shiru yayi yana kallonta, saikuma ahankali yakai hannunshi yacire glasses din idanunshi yace "Ammi baki gaji da kiran mutumin nan ba eh?" dan murmushi tayi dakana ganin murmushin kasan na damuwa ne tace "inaso na sanar dashi zamu dawo Abuja ne dama, kaga yakamata yazo yaduba mahaifinshi baida lafiya fa" cikin dan bacin rai yace " Ammi yafiki sanin mahaifinshi baida lafiya idan baizoba ki shareshi shiya sani, Ammi kidena sa kanki a damuwa, what if u fall sick eh? ina zansa kaina" tunda take maganan take kallonshi, ganin ranshi yabaci na damuwa yasa tai murmushi tace "wayagaya maka ina cikin damuwa eh, I'm fine kawai dama sabida Dadda kane nadamu, oya maida glasses dinka kafo kyau ahaka, mata sukaga this ur no nonsense eyes bazasuyi approaching dana sunce suna sonshi ba" dan murmushi yamata daya karamai wani irin kyau saka glasses din tayi tace "oya muje to, come here lemme hold ur hand asan nine maman this handsome boy" turobaki yayi yace "Ammi kindaiga akwai yara anan ko karkisa su rainani" yay maganan yawuce dasauri kafin tarikeshi zuwa wajen Sharif dakechan, binshi da kallo tayi saikuma takarasa inda su Aneesa suke tace "let's go girls gobe sai makaranta" duk dariya sukayi, Aneesa tace "Ammi kince zakicema Ya Asad ya chanza min waya in munkai" gyadamata kai Mami tayi tace "eh dukanku zansa ya chanza muku" ganin Sharif namusu waving hannu yasa Ammi tace "kumuje" wucewa sukayi saba ko 3min basuyiba sukai boarding jirginsu zuwa Abuja. Suna sauka airport motoci biyu sukazo dukansu, shiga sukayi yayi Ammi takalli Asad dake kusada ita tace "gobe zaka fara shirye shiryen aiki ko" gyadamata kai yayi yace "eh gobe ne, illustrator dinmu Ammi yasami accident a hannunshi I don't know how am gonna start looking for new one, gawanan TV program dinan dazan fara dukshi yabatamin schedule" ahankali tace "don't worry komi zai daidaita I trust my son" harsuka karasa anguwansu, wani hadadden gida aka bude musu shiga sukayi gidan ya bala'in hadu, sassakowa sukayi Security gidan nashiga da kayansu ciki shikuma yay hanyar flat dinsu, binshi da kallo Aneesa data fito daga motansu tayi, fitowa Mariya tayi tace "yarinya kin debo ruwan dafa kanki" juyowa tayi takalli Mariyan cikeda tsiwa tace "mekike nufi?" Ammi dahartai gaba tajuyo ta kallesu tace "to bismillah tsiya zata fara ne" dasauri Aneesa tace "Ammi Mariya ke tsokana na fa" murmushi Ammi tayi tace "barta kinji Aneesa zomuje" dasauri Aneesa tabita tanama Mariyan gwalo itakuma tai dariya zata mata gwalo Rahima ta ture mata meya tace "dalla wuce mutafi" wucewa tayi tana turo mata baki sukai flat dinsu. Hadadden Babban falo ne dayaji komi na duniya, stairs sukayi, sukai dakinsu daya hadu sosai irin dakin mata Ammi tashiga dakinta, ahankali ta ijiye handbag dinta tazauna kan gado tai shiru saikuma tamika hannunta tadauko wayanta dake cikin handbag din tai dialing number datai saving da my husband, har wayan tai ringing ta katse ba'a dagaba, sake dialing number tayi wayan na gabda tsinkewa aka dauka dasauri tace "Alhaji wanan wani kalan haline kakeyi? children are all at home, Asad is back yau kusan 5days kenan ina kiranka baka dauka what is all this Alhaji bazaka zo kaduba iyalanka ba? Eh?" muryan mace taji tawanija tsaki mtswwww..... cikin muryanta dayakedan shake da alamu bacci suke tace "dalla Malama karki sake kiran number nan kinwani hana mutane bacci, yabaki kudi yasaki gida mai kyau, aikinki shine zaman gida u are a house wife, ki kulada gidanshi da yaran kanninshi daya mutu that's ur work and leave him alone, yana nan ina kula dashi, ki ganshi nan ma bakinshi kan tsayayyun nonuwana yana tsotsa yana bacci ba irin naki ba daya koma kaman silipas" wani irin tari Ammi tashigayi batasan lokacin data yarda wayan akasa ba yafadi kuka taji tanaji but batason yaranta suji tana kuka ko su ganta jitayi duniyan tamata zafi dasauri ta tashi bude kofan dakin tayi tafita sauka kasa tayi tafice compound security na ganinta yabude mata kofa murmushi dole tamai tace "idan yarana na nemana tell them nashiga wajen Hajiya, Mamana" Gyadamata kai yayi yace "yes ma" fita daga Gate din tayi, ko tafiyan kafa goma batayiba ta tsaya gaban gate din gidan dake gaban nasu, knocking tayi security gidan yabude kofa yana ganinta yace "welcome back Ma" murmushi tayi tace "is Hajiya around" "yes she is" dasauri tashiga gidan direct kofa tabude tashiga Hajiya na zaune kan kujera tana duba wani magazine idanunta da glass sai yar aikinta dake goge TV stand, jin sallama yasa tadago kanta takalli Ammi datai sallaman, fadada murmushin fuskanta tace "Walida" ahankali muryanta narawa sosai tace "Haj.....iya" tashi Hajiya tayi dasauri ahankali takaraso gaban kofan tana kallon fuskan Ammi ganin yanda idanunta suka cicciko da hawaye yasa takama hannunta tace "muje sama" tana rikeda ita sukai sama har zuwa dakin Hajiya, shigarda ita ciki tayi sanan tamaida kofan tarufe kafin ahankali takama hannunta ta zaunar da ita kan gadonta tace "ya isa Walida ya isa" wani irin rungume Hajiya tayi gam, duk duniyan nan batada wacce tarike amatsayin uwa sai Hajiya, saisa babu abinda take boyemata, Hajiya bata hanata kukan ba saidai bubbuga mata batada takeyi ahankali tace "it's okay ya isa" tadade ahaka sanan tadago kanta, tissue Hajiya tabata fuskanta tashiga sharewa tace "Hajiya babu narasa Yaya zanyi da Baban Asad, gabaki daya baida lokacin iyalinshi, har muje kano munyi sati mudawo mutumin nan baizo yaduba mahaifinshi ba, yana nan Abuja fa amman yakauracewa gidanshi, kullum ina cikin yima yara karyane yay tafiya wanan kasan yay tafiya wanchan kasan, Hajiya Asad danshi ya tsani mahaifinshi sama da komi, kinsan bakin halin Asad koyaya naso nawanke mahaifinshi bayama yarda bama ya saurarena, nasan Asad kadai na haifa wlh Hajiya ke shaida ce anan falon ki ranan nace na yarda ya karo aure ba hanashi kara aure ba, Hajiya yaki sai bin matan banza, kince idan naje kano nabada sanarwa masallatai asashi a addu'a wlh duk nayi, baya daukan wayana yanzun nan nakirashi wata karuwanshi ce tadauka, I don't know what to do Hajiya, ina zansa raina inji dadi eh? Baban Asad yana girma yanakara tambarewa shekaranshi 60 fa yanzu". 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR Free Page EPISODE 1️⃣5️⃣ Hannu Hajiya tasa cikeda tausayinta tace "stop crying, dena kuka, ya isa" tasata ajikinta tana bubbuga bayanta tana gayamata kalamai masu sa natsuwa hartai shiru, saida ta natsu sanan Hajiya tace "bari nakawo miki abinci kici nasan is being long bakisa abinci acikin nan naki ba" batama tsaya sauraronta ba tawuce tafita, lafiyayyen tuwo takawo mata da miyan kubewa busassa da kifi da man shanu, bude kofa tayi tashigo dakin tana kallonta, maida kofan tayi tarufe takaraso ijiye tray tayi akan carpet tace "wayyo jikin tsufa, sako kici kinga kinsani aiki" murmushi tayi ahankali sanan tasauko tasan halin Hajiya hakan yasa batai gaddama ba tashiga cin tuwon sosai taci tuwon ta koshi sanan taje tawanko hannunta anayi tafito carpet din Hajiya tanuna mata hakan yasa tazo tazauna kusada ita, ahankali Hajiya tace "Walida, ke yanzu ba yarinya bace, inda ace Asad yayi aure da yanzu kinada jikoki dozen ma halan" dan murmushi tayi Hajiya tace "my point is indai rayuwan zaman aure ne you've come a long way saidai kibama wasu shawara, kunada yaro dakeda shekaru 33 aduniya aiko littafi aka baki zaki iya rubutawa kan zaman aure, Baban Asad wanan halin nashi bayau ko jiya yafara ba, kinyi kuka kinyi kuka Walida, kukan jini ne kawai yarage bakiyiba, kinsan yanayin lafiyanki, amatasayina na mahaifiya agareki dudda bani na haifeki ba abinda nafadi miki kafin kutafi kano shizan kara gayamiki ki manta da batun mijinki and concentrate akan yaranki, fi fawwalama Allah lamarin Baban Asad kidinga mishi addu'a idan yanada rabon shiriya wlh zai shiryu, kinsan yanda Asad ke sonki sama da rayuwanshi ko ciwon kai yaron nan yaga kinayi lamarin shi saiya tabarbare yaron dayakeda TV show dazai fara nan da kwana biyu, I think, kinason ya susuce ne"? Dasauri Ammi tace "a'a Hajiya" "then dole ki jajirce ki kauda komi, Alhamdulillah baihanaki ci ba baihanaki shaba, ke kodama yahanaki danki Allah ya horemai mezai dameki, ki share batun shi yanda yasa kafafunshi yafita dakanshi zaisasu kuma yadawo gidan kinji" harcikin ranta taji wani sanyi wani zubin takance inama ita yar Hajiya ce, dan Hajiya tayi arayuwa, tadauketa tamkar yar cikinta, haka tadauki yaranta tundaga su Asad da Sharif harzuwa kansu Aneesa kaman jikokinta, babu abinda abinda take iyayi bata sanar da itaba, murmushi tayi ahankali tace "Hajiya nagode, Dadda da Turai sunce na gaisheki" haba Hajiya takama tace "wanan rigimammen tsohon yanzu bai biyoku yadawo nan Abuja yadinga ganin specialist bako" dariya tayi kaman ba itane tasha kuka ba tace "ai yace shi kano yakeso, Turai natare dashi dakuma Nurse dinshi, ya samu lafiya sosai kafin mudawo ma" Hajiya tace "Masha Allah". "Grandmaaa" Du'a data shigo falon takira Hajiya ganin bata falo, shigowa Razika dake biyeda ita tayi tace "tana sama, muje kinuna mata kalban da aka miki" dasauri Du'a tai stairs tana murmushi sosai dan kitson da aka mata yamata kyau dan ba'a taba yimata kalanshi ba, tana kaiwa falon sama takara kiranta. "Grandma" dasauri Hajiya take tareda Ammi tace "jikata tazo bangayamiki ba, Du'a gani nan adaki shigo" bude kofan dakin Grandma ahankali tayi tashigo Razika biyeda ita, ganin wata babbar mace baka tareda Grandma yasa ta tsaya batare data karaso ba, saukar da kanta tayi kasa ahankali ta gaida matar tace "ina yini" murmushi Hajiya tayi takalli Ammi tace "ana gaidake" wani kayataccen murmushi Ammi tayi tace "Masha Allah, sabida kin ganni kikaki karasowa ciki wajen Grandma dinki" dan murmushi Du'a tayi cikeda kunya ta girgixa kai saikuma tajuya dasauri tace "bye Grandma" sanan tabi ta gefen Razika tafice dasauri, dan dariya Hajiya tayi tace "kinganta haka take akwai kunya" takalli Razika tace "anmata kitson" gyadamata kai tayi tace "anyi kalba akayi, yayi kyau sosai" "haka nakeso, jeki bata abinci taci" ficewa Razika tayi, Ammi tace "Hajiya yar Muktar din UK ne" dariyan manya Hajiya tayi tace "yar Zainab din kano ce, Du'a, wacce nake baki labarinta" murmushi Ammi tayi tace "Allah sarki Yarinyar ga kyau ga natsuwa" Saida tai wanka sanan ta chanza kaya zuwa wani gown data dauka daga wardrobe red iya guiwa ya tsaya mata yamata kyau, bata daura dankwali ba tasaki kalaban dayake nan har waist dinta kaman ansaka mata attachment tabude kofa tafito da saurinta ta sauko dan itada Razika sun biya wani super market tadauki drawing book babba da HB Pencils da eraser da colors, dakin kasa wanda shine dakin Razika da Amina ta shiga suna zaune sunacin abinci duk suka bitada kallo ganinta adakinsu, Razika ta kalla tace "ina drawing book dina"? Dan ware ido Razika tayi sanan tace "inama nasa ohh natuna suna dinning" dasaurinta harda dan gudunta tawuce tafita a dinning ta tsaya ganin komi yasa tasaki wani murmushi she's so happy and excited bayan reading novels wanda technically Ya Hamad ne yakoya mata the only thing datasan ta iya shine zane, babu abinda bata iya zanawa ba saida yawanci abinda tafi zanawa yanzu shine takalma tana bala'in son zama takalma sabida batada takalma agida dayawa dan bata fita saisa hakanan idan tazauna saita dinga zama dream shoes dinta. fitowa tayi tazauna akan falon, bude komi tayi, tai sharpening pencil dinta sanan tabude hadadden drawing book din da Razika tasiya mata ta shiga zane, yanda take zanen kadai saika tsaya kana kallon hannunta sabida wani kalan burgewa datake yi kafin good 3min tagama zama wani tsantsararren takalmi hill na mata, murmushi tayi tadauki drawing book din tana kallon takalmin saikuma chan ta hura iska sabida all particles na eraser dakekai yafita sanan tace "to yanzu wani suna zansa maka kai takalmin nan kaga nadade banyi drawing ba tunda drawing book dina na gida yacika Ya Hamad baikara sayomin ba" shiru tayi tana tunani kawai saita sauke drawing book din akano saitama zanen tittle Du'aXAbuja, kallon rubutun tayi dayay kyau, kawai saita bude wani page tashiga zana wani daban. Ahankali Ammi datai sallama da Hajiya ke tafiya kan stairs Hajiya bata rakota ba sabida wani office related call da aka mata, tundaga stairs take kallon Du'a, dudda batasan metake zanawa ba but ganin drawing book yasan tasan zane take, kitson kan yarinyar tabi da kallo da yanda take zane ita kadai saita daga ta kalla tai murmushi tasauke tacigaba, hakanan Allah mai daurama mutum so da ki kawai taji Du'a na burgeta tanason yarinyar, karasa saukowa tayi Du'a ma bataji saukowanta ba sabida yanda hankalinta yay nisa, karasawa cikin falon Ammi tayi ta tsaya tana kallon takalmin da Du'a ke zanawa batasan lokacin datace. "Masha Allah, you are gifted Du'a" dasauri Du'a tadago kanta ta kalli Ammi, murmushi tayi sosai tace "Mum yayi kyau"? Hakanan Ammi batasan mesa ba but kiranta da yarinyar tayida Mum yasa son datake mata ma yay double da sauri tazauna kan kujeran dake gefen Du'a tamika mata hannu tace "bani drawing book din naga" da sauri Du'a tadauki drawing book din tamika mata sanan ta matso kusada kafan Ammi ta daura hannayenta kan cinyan Ammi batare datama sani ba tana kara leka drawing din itama, gyara zama Ammi tayi jin yanda yarinyar ta dagata tafara duba drawing din daga farko tace "wow, haka kika iya zane Du'a, this is talent wlh" murmushi tayi sosai dan batasaba ayabeta ba agidansu Ya Hamad ne kawai yake cewa zanen ta yay kyau, murmushi takara yi tace "Ya Hamad ne kadai yataba cewa inada talent sai ke Mum" takarashe maganan looking damn happy dayasa Ammi taji suka matsalolinta ma sukau, hannunta takai tashafa kan Du'a tace "you are very very talented Du'a, kinsan nawa ake biyan wayanda suka iya zama abu haka" girgixa mata kai Du'a tayi tana kallon Ammi saikuma tace "Mum ni ai baza'a biyani ba, kinga banyi school ba a JSS2 na tsaya, wanda yay karatu ne ai ake bashi aiki ko"? tunda take maganan Ammi ke kallon yarinyar, idan tana magana sosai zakaga rashin wayau da yarinta aciki wanda yarinyar dakeda shekarunta bai kamata ace hakan yasameta ba, murmushi Ammi tayi tace "ko ina talent yake yanada kyau ayi acknowledge nashi, and it doesn't matter sabida kin tsaya da karatu a JSS2, with this" Ammi tanuna mata drawing book din tace "with this zaki iya samin aiki a companies da dama that are into shoes kuma abiyaki" wani irin kyalkyacewa da dariya Du'a tayi tawani kife kanta akan kafan Ammi tanajin dadi sosai data kasa boyewa dayasa Ammi takarajin tashiga ranta, Hajiya data dade a stairs tana jinsu takaraso tazauna kan kujera tace "ke karki karya ma mata cinya inba so kike Asad yashigo yay yaki dani ba kirufamin asiri yaron nan son maman shi yake kaman me" dariya sosai Ammi tayi tace "kundai fi kusa kedashi Hajiya" tashi Du'a tayi tana murmushi itama, Ammi tace "how about natafi da wanan drawing book din sabida nasaman miki aiki dashi" dawani irin sauri ta gyadamata kai tace "eh Mum kutafi dashi" tawani washe baki tajuya tana kallon Hajiya dake kallonsu itama tana murmushi tace "iyye Du'an baaa, tobazakima Mum din naki godiya ba za'a neman miki aiki kinata washe baki" cikeda farin ciki takalli Ammi tace "Mum nagode Allah amfana" tashi Ammi tayi rikeda drawing book din tace "bari nashiga gida" Takalli Du'a tace "yaushe to zakizo ki gaidani agida inada yammata nima kinga saikiyi sababbin kawaye ko" juyawa tayi takalli Hajiya dake kallonta tace "yo jama'a kome aka tambayi yarinya sai tajuyo takalleni, Razika da Shemau sa rakota suzo gobe" "shikenan, Hajiya sai munyi waya" "tom Walida ki gaidamin da Sharif dasu Aneesa, shikuma gogan kice nace Allah yataroshi" dariya Ammi tayi tana bude kofa tace "yau dai munjiku arana kuda ba'a shiga tsakanin ku" Jan kofan tayi tarufe tafice. Hajiya ta kalli Du'a daketa murna tace "zansa driver yasayo miki wani sabon drawing book, kinci abinci"? girgizamatakai tayi tace "a'a" dasauri tana hararanta tace "tashi kije kici abinci banson kina wasa dacin abinci, anjima idan zasuyi girkin dare saiki bisu kidinga ganin yanda sukeyi ko" murmushi tayi looking so happy tace "tom grandma" sanan ta tashi tayi dinning dasauri Grandma tabita da kallo daga zuwanta harta fara murmurewa kwanan nan zatai kiba tai kyau abinta. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 1️⃣6️⃣ Koda Ammi ta shiga gidan Sharif kawai tagani zaune a dinning yanacin spaghetti da Rahima tadafa, yana ganinta yace "Ammi ina kikaje" zama tayi akan dinning tace "daga wajen Hajiya nake" takalli Rahima data fito daga kitchen tace "iyye yammata na angirma harkinyi girki" murmushi tayi tazauna kusada Ammi ashagwabe tace "Ammi please sai next Monday zamu resuming school this week muhuta muyi shopping kinji Ammi" Sharif dakecin abinci ne yaharareta yace "why mesa yaran this generation basason school saison kula samari" murmushi Ammi tayi takalleta tace "bazakuyi lectures bane" ahankali tace "first week lectures baya serious sosai Ammi fa"gyadamata kai Ammi tayi cikeda gamsuwa tace "okay I will think about it inasu Aneesa da Mariya"? tabe baki tayi tanajan plate tace "sunyi bacci" kallon Sharif dayagama cin abinci Ammi tayi tace "ina Asad" ajiye cup din dayake shan ruwan dashi yayi yace "dazun nan yafita, bansan inda yajeba" "Ammi wai yaushe Daddy zai dawo" Rahima dake kusada Ammi tamata tambayan, murmushi Ammi ta kakalo tace "this week ko next week, bari kiga naje na kwanta" ta tashi tawuce sama Sharif yabita da kallo. Wani dankareren building wanda nan a offices din senators na Nigeria suke ya dumfara cikin mad ride dinshi na Benz, tsayarda shi sojojin dake guiding building din sukayi, ahankali yasaukar da glass din motar, ganin wanda keciki yasa suka shiga gaidashi, Jan motar yayi ciki har zuwa inda ake parking yay parking sanan ya kashe motar yafito, wanan karan yana sanye cikin wani classic 3quater wanda dakadan yawuce gwuiwanshi dark blue color, sai wata white t shirt mai V neck dayasaka data kara fitar da kyawunshi kana iya hango kwantaccen gashin kirjinshi ta wuyan rigan sabida shape din dayake dashi na V, kafanshi Sanye cikin flat slippers na Gucci, kanshi ya sanya p cap na Gucci, lips dinan nashi yay pink yir looking damn moist and fluffy, sai black eye glasses na Gucci a idanunshi, hannunshi ya daura agogo da bracelet na Rolex akai sai zuba uban kamshi yake, kana ganin shi kaga irin yaran masu kudin nan yan gayu looking casual sabida yau Sunday, maida kofan motan yayi yarufe sanan yafara tafiya ahankali yashiga cikin premises din babu kowa ciki sai security personnel dake gadin wajen wanda dazaran sunganshi gaidashi suke dan sunsan koshi waye, elevator ya shiga zuwa 5 floor, wanda yasadashi dawani mahaukacin building dazaki dauka ataurai ne, ga kujeru na ma'aikata amman sabida yau Sunday babu kowa, cigaba yayi da tafiya zuwa gaban wani hadadden kofa wanda da finger print ake bude kofan, baiyi yatsanshi yasa abin yayi magana Authorize Mr Asad, kama handle din kofan yayi yatura kofan yashiga tashi daya, wani irin zabura mutumin yayi yasauka dagakan yarinyar dayakekai dataji uban attachment ja akai yanajan boxer dinshi dayadan sauke kasa kadan dama dagudu yana rufe abin datai wani automatic kwanciya jikinshi na mugun bari yakalli yarinyar da babu kaya ajikinta yana mata ihu. "leave this office, I said leave" Ahankali yaja kafanshi baya kadan bazaka taba iya tantance wani yanayi yakeba sabida glasses din dake kan idanunshi, dasauri mutumin daya rude yace "Asad look is not what u are think......" awani irin zuciya Asad yajuya fuuuuu, dagudu mutumin yashiga laluban kayanshi yana sakawa batare dayabi takan karuwanshi dake sa kayanta arude ba yasa riganshi baima tsaya saka malum malum ba yazura slippers din office yafice dagudu, sauka kasa yayi gudun da yakeyi yasa yacimmai shan gabanshi yayi yace "Asad listen to me listen to me son please" tsayawa yayi chak yana kallon mahaifin nashi dat so much disgust him now, ahankali yakai hannunshi yacire glasses din dake kan idanun nashi yace "wanan ne US din dakaje ko Dad? Almost 2month babu wanda yasaka a ido kana garin nan Dad" juyawa mutumin yayi yana kalle kalle ganin babu mutane inda suke yasa cikin muryan lallashi yace "listen to me Asad wlh naje US ba karya nayi ba kawaidai dana dawo banje gida bane" wani irin kallon mahaifin nashi yake kallon bakin ciki da tsantsan tsana, Dan murmushi mahaifin nashi yayi irin na marasa gaskiya, cikeda lallashi yace "how are you my boy? Your Mum told me kadawo kaima kaje kano gaida Dadda ka, sanan zakai hosting show ma Youth a TV station, I am so proud of you Asad dina, you are really my son" sosai idanunshi sukai ja ruwa yacika a idanunshi fall ahankali yace "why are you doing this to Ammi? After all the sacrifice da Ammi tamaka why are you treating her this way, why are you maltreating my Mum Dad eh"? kana ganin yanda yayi maganan kasan zuciyanshi namai zafi da daci, ganin yanayinshi yasa Baban yadan sosakai yace "listen Asad, inamaka kallon yaro but I think u are not more a little boy anymore, I love you morethan anything in this world, in fact ma darajan kane ma yasa nai deciding I will leave tareda mamanka har karshen rayuwa but banason mamanka Asad, ko kadan bani sonta, auren hadi akamana nida ita, ur Mum was never my choice, choice din Daddan kane, yar maigadin shine dayarasu dagashi har matanshi lokacin sunje gida kauye suna dawowa suka sami hatsari suka rasu, shine sabida how the gateman was good to Daddan ka yasa yadauki maman ka shida Mamana Allah yajikanta suka raini mamanka aka sata a makaranta aka hadani aure da ita dudda na nuna banso..." yanda idanun Asad sukaija zaka dauka zai makance ne, cikin wata irin murya datai rauni bama ta fita sosai tsabagen bakin ciki da kunci yace "is that the reason why kakebin all kind of useless matan banzan Abuja nan Dad" Dasauri yace "banason aure aure, da mata daya zan iya rayuwa since uwarka ce d lucky one saisa I am stuck with her, look son I don't wanna go into details with you now, nan gaba u will understand after all kai d'ana ne, my blood runs through ur veins, you are just like me" cikin wani irin huge voice yace "I will never be like you, bazan taba zama mutum irin ka ba, I despise you Dad, u are nothing but a shame to my name, wlh da ana chanza uba dana chanza ka cus u don't deserve a son like me much less a good wife kaman Ammi na" yana maganan yawuce yabude motan shi yashiga yana kokarin tadawa Dad yazo wajen. "Asad, Asad, come here son calm down nasan ranka abace yake, but yakakeson nayi eh ur Mum is such an old school babu abinda ta iya sai kunya, Asad" wani irin jan motanshi Asad yayi yabar wajen ubanshi na kwalamai kira. "Asad, Asad" tsaki yaja yadafa kanshi yace "yaro sai bakin zuciya, nima maiya kaini zuwa office yau" tsaki yayi shi kadai yace "to nasan zaizone yaron da fushi yake dani kona kirashi baya dauka" tsaki yasakeyi dukya bala'in damu yace "daka tsaya kajira Zinariyan ka daganan ma kona sami contact din kyakkyawan yarinyar nan dayafimin, yanzu look what I cause yanzu, shiit yanzu sai nakoma wajen wanan matar nan da nonuwan kirjinta sunfi silifas tsawo abu har cinya, dan Allah dai jibi nonon wanan cinyare dinan atsaye, na Zinariya ma haka, amman ace yaro yakasa ganewa uwarshi ba gaba ba baya gatanan ne gabaki dayanta zero ce" yaja tsaki yawuce yana tafiya zuwa ciki ranshi fall da damuwa. Allah da ikonsa ne kawai yakawoshi gida lafiya, ko parking din kirki bai iya yayi ba yafito daga motan dawani irin gudu security su yace "subhanallah" ganin motan na tafiya yashiga yay parking da kyau shikuma Asad yay wucewan shi batare dayama juyoba, ko katon Sharif dake zaune a garden dake kusada flat dinsu baiyiba yawani irin buga kofa yashiga ciki, binshi da kallo Sharif yayi saikuma ahankali yasauke ijiyan zuciya yacigaba da aikin dayake yi akan system, karan zubarda abu dayaji yasa yatashi da sauri ya ijiye system dinshi awajen, bude kofa yayi yashiga falonsu sanan yamaida kofan yarufe yay kitchen dinsu da sauri tsayawa yayi awajen kofa yana kallon yanda Asad ke zubarda komi na kitchen din yana rotsasu akasa kaman wanda yazare, cikeda damuwa Sharif yace "what's wrong with u Asad"? Wani irin daga kafa Asad yayi yadaki fridge din kitchen din cikin zafin harshe yace "it's none of your business leave me alone Sharif" shiru Sharif yayi yana kallonshi yanda yake haukanshi shi kadai wanda is not new to him, kowa yasan Asad da zafin zuciya haka Ammi ta haifoshi da halin nan. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR Freepage EPISODE 1️⃣7️⃣ Yagama barinshi duk basu isheshi ba ganin yafara punching kofa da hannunshi yasa dasauri Sharif yashiga kitchen din wani irin kamashi Sharif yayi yasashi ajikinshi ya rungume tsam yace "calm down Asad ba Ammi tace idan ranka yabaci kadinga salati ba, calm down please" kokarin fizge kanshi yake yana ihu. "I said leave me alone Sharif, stay out of this" kankameshi sosai Sharif yayi with all the power he got yace "Ya isa Asad I am here for u, I am here, we gonna be brothers forever okay, ina kaje? what happen? Giran da kayi dazu ina kaje?" shiru yayi yakasa magana ahankali Sharif yace "you went to see Dad ko"?Murya chan kasa yace "I guess kaima kasan babu wani US din dayaje" shiru Sharif yayi sai chan yace "before muje kano lokacin kana UK I saw how worried Ammi is yasa naje office naduba shi, I saw him though shi baiganni ba baisan naganshi ba" shiru Asad yayi saikuma gently yatashi daga jikin Sharif zama yayi akasa ahankali yajingina da cabinet din kitchen din idanunshi sunyi jajir, zama shima Sharif yayi kusadashi yana kallon kasan wajen, ahankali Asad yace "I don't know why Dad choose this life he's 60 but jin kanshi yake kaman dan 20, that Oldman is lost Sharif completely, can u believe niyake gayawa I am just like him eh Sharif" yay dan shiru idanunshi sunyi ja yace "I can never be like that man, bazan taba neman matan banza ba, wlh bazan tababa cus I hate them kyama ma suke bani, I hate that I am his son, wlh da ana chanza uba da na chanza nawa, I hate that man Sharif" kallonshi Sharif yake bakaramin tausayi yabashi ba matsawa yayi kusada shi ya jingina da cabinet shima yace "bazaka taba zama kaman shiba that I am sure of Asad but we gonna do something right now" yay maganan ahankali yace "inaso ka share batun Dad for now dan is affecting u physically and mentally bayan kasan u need to be at ur best gobe zaka fara TV show dinka eh Asad, this whole mess will affect ur productivity as well as ur performance, I cannot be managing everything for u eh, u need to be at ur best mugama this TV program in the next 7days sabida kasamu muyi concentrating a office we need to release new collection eh Asad, banda ma haka kanason Ammi taganka ahaka ne kaga how I am better than u kenan, tunkafin mutafi kano nasan Dad na garin nan amman koda wasa ban nunama Ammi ba sabida I need her happy, kaiko look at u now bayan kasan mu Ammi ke gani taji dadi common be a man for Ammi, let's keep pretending we don't know what Dad has been up to koma yana gari" Ahankali yasaki dan murmushi saiya kalli Sharif din yace "kasami wanan illustrator din?" girgizamai kai yayi yace "no he's on his summer break wai, kaima I don't get u Asad why don't u wanna give Nigerians dinmu a chance" "cus they can't give me what I want" hararanshi Sharif yayi yace "shikenan haka zan zuba idanu inta kallonka wlh idan ka shiga tight corner kaida kanka zaka dinga neman su" tashi yayi ahankali yace "don't worry I will get one" fita yayi daga kitchen din Sharif yabishi da kallo cikeda so dakuma tausayin dan uwan nashi yasan wani zubin Allah kan jarabci yara da iyayensu and that's Asad da dukansu ma a family nan biggest test, Dad gashinan ne kawai living one kind of useless life kaman yaro, imagine Babba dashi he is willing yayi karya yabar gidanshi da sunan yatafi UK just dan yatafi wajen matan banzan shi, tsohon mahaifinshi baida lpy he don't care yaje yaduba shi saidai yayta tura kudin magungunan shi, ayanzu kuma shi kadai ne dandan Dadda namiji, dan dama Dad ne Babba sai mahaifinsu daya rasu, sai Anty Turai mahaifiyar Aneesa, Mahaifinsu daya rasu ne kawai ya haifi yara dayawa a family Shine first born sai Rahima sai Mariya, itakuma Aneesa ita kadaice yar Mamanta Turai, da mijinta yasakota tadaukota suka dawo gidan Dadda dazama kafin tabama Ammi ita aka zo da ita Abuja tafara school gudun kar mijin ya kwace ta dan Anty Turai yar rigima ce fitinanniya saisa ma takasa zaman gidan miji. Banda haka Ammi is just the best woman aduniyan nan, sosai take tarbiyan yaran batare data nuna gazawanta ko gajiyanta ba, hasalima bala'in son yaran take suma haka suke sonta dan wajen Ammi yafi musu ko'ina. Mikewa Sharif yayi ahankali yanabin kitchen din da kallo, kwashe abubuwan dabasu wani baci sosai ba yayi sanan yawuce yafita, sama yayi ahankali yabude kofar dakin Asad din, akan gadonshi ya ganshi yana bacci, ajiyan zuciya yasauke sanan yaja kofan yarufe yasauko kasa, masu gyaran gidansu yakira yasasu gyara kitchen din sanan yakoma falon sama yazauna tunawa ma yayi da system dinshi awaje dasauri yatashi yawuce waje. Dayake tanada yammata hakan yasa Ammi bata dauki yan aiki ba, su take sawa girki, duk tana kitchen taredasu suna aiki takalli Aneesa dake wanke rice tace "namuku kawa fa" dasauri duka yaran suka tsaya suna kallonta, Aneesa ce tace "Ammi a ina"? murmushi Ammi tayi tana maida marfin tukunyan data bude tana rufewa tace "jikan Hajiya ce, sunanta Du'a, she will be ur mate Aneesa keda Mariya" tanuna Mariya da itama ta tsayar da peeling Irish din datake tana kallon Ammi, tafi Aneesa tayi da Mariya tace "yi sauri Mari mugama girki muje gidan Hajiya" murmushi Ammi tayi takalli Rahima data cigaba da aikinta tace "Anty Rahima kinyi shiru" wani irin murmushi tayi tace "Ammi bakina Ya Asad maganan wayoyin muba" dasauri sauran sukace eh Ammi, hararansu tayi tace "wai mesa kuke tsoron yayan ku haka, aiko babu wanda zai kara aikena wajenshi cikinku kuje kusameshi dakanku kokuma kuma Sharif magana yasaimuku" dasauri Mariya ashagwabe tace "Ammi wlh Ya Sharif mugune yace wai babu wanda zaici kudinshi cikinmu wai tara kudin aure yake, duk wanan wahalan inda Dad na nan muna gayamai zai sai mana wlh" shiru Ammi tayi tace "kugama girki kuje ku sami Asad to baruwana kudena sani a lamarin ku" nariga nahada muku komi ku karasa kuyi setting dinning up tai maganan tana fita daga dakin. Wuraren 5 suka gama girkin tass sukai setting dinning dakinsu sukayi kowa yay wanka, Aneesa data gama shiryawa cikin wata yar rigan zaman gida half gown mai spaghetti hand ya tsaya mata a knee ta kallesu tace "kumuje wajen Ya Asad" kwalalo ido daga Mari har Rahima sukayi atare sukace "kidawo lpy nidai bazani ba" hararan su tayi tace "wlh naje nawa kadai zan fadamai" tawuce fuuu tafice tana tafiya ahankali gabanta nafaduwa, tsayawa tayi takalli kanta a madubin dake bangon falonsu tayi kyau sosai ga kitson kanta yamata kyau abunku da faran yarinya dan gidan Asad ne kawai black cikin yaran, bude kofa tayi tai flat dinsu Asad, tsayawa tayi abakin kofan tai knocking, jin ba'a amsaba yasa ta danna door bell har sau biyu, sake knocking tayi cikin wata irin isasshiyar murya akace. "waye"? faduwa gabanta yayi muryanta har rawa yake tace "Ya Asad is me, Aneesa" shiru aka sakeyi takai kusan 3min atsaye awurin sanan akace "come in" dasauri tabude kofan ta shiga yana zaune a falo dagashi sai towel daya daura a waist dinshi ya zaunar akan kujera ya mikarda kafa yadaura kan enter table yadaura MacBook akan cinyanshi yana aiki ruwan coily gashinshi nabin fuskanshi. Kallo daya tamai tasaukar da kanta kasa dasauri, tunda take bata taba ganinshi ba rigaba sai yau, wani irin hadiye miyau tayi gabanta na dukan uku uku, tashiga wasa da yatsunta takasa magana, batare daya kalleta ba hankalinshi nakan aikin dayake yi akan system yace "why are you here"? Yanda kirjinta ke dukan uku uku yasa muryanta yama fara rawa tace "Y.....a As...ad, dama....dama...." saita karayin shiru tadan dagokai ta kalleshi aikinshi yakeyi comfortably a MacBook dinshi kaman baimasan tana wajenba, kirjinshi tabida kallo jitayi jikinta yadau rawa da sauri ta maida kanta kasa tadage tace "Ya Asad I want a new phone Ammi tace zata gayama shine yanzu wai muje musameka da kanmu, ahhmm kuma da shopping da resuming school, I want new school bags, pairs of shoes sai Abaya dakuma and kuma pads dinmu yakare duka" saida takai nan tai shiru kirjinta na bugawa fat fat fat bata taba sanin zata iyama Asad magana ba saiyau, juyoda kanshi yayi yakalleta for the first time tunda tashigo dakin, ahankali kaman baison yay maganan yace "what happen to your phone" dagokanta tayi ta kalleshi yanda yake kallonta yasa takasa mai karya langabar da murya tayi tace "babu abinda yasame shi I just wanted a new one" still kallonta yake babu alamun wasa kowani yanayi akan fuskanshi yace "and the other things nawa zai isheki kisaya" wani irin murmushi tamai cikeda jin dadi tace "150k zai isheni Ya Asad" Su Rahima da tuntuni suke gaban dakin suna jiran suji yanda zata kaya jin yana tambayanta nawa yasa suka turo kofan suka shigo suna sallama, duk atare suka gaidashi muryansu narawa. "Ya Asad good evening" dasauri Aneesa tace "Ya Asad kaga saida nace musu fa suzo muje tare sukaki wai tsoro sukeji sai yanzu dasukaji zaka bani kuma wlh ni bazan raba kudina daku na nawa kadai nafadi" dasauri Rahima tadan kyafta mata ido takalli Asad din tace "Ya Asad sorry" Mari ma ahankali tace "Ya Asad sorry ni wlh tsoro ya hanani ma biyota" duk tsayawa yayi yana kallonsu yanda duk suke trembling, ahankali yasaki dan murmushi, wani kalan dadi ne yakashe su dasauri Rahima tace "Ya Asad nima I want new phone" dasauri Mariya tace "Ya Asad nima" ganin suna neman samai ciwon kai yasa yakalli Aneesa yace "go to my room, check the left sidebed drawer bring all the money that is there" wani irin dadi taji tace "tom Ya Asad" dasauri tawuce stairs tai sama dakinshi tabude ta shiga wani kamshi ne yamata sallama, drawer taje ta kwaso duka kudin wrappers na yan dubu dubu ne guda 10, kwaso su tayi tasauko, Su Rahima na ganinta suka shiga murmushi, gabanshi tazo zata bashi kudin gefenshi ya nuna mata hakan yasa ta ijiye kudaden awajen, hannu yasa yadauki rapa biyu yabata dasauri takarba tawani washemai baki tama kasa godiya, "Rahima" "na'am Ya Asad" dasauri tazo dauka biyu yayi yabata dagudu Mari tazo itama yabata biyu dukansu yabasu 200k each, ahankali yace "u will get the phones tommorow" wani irin ihu sukayi sukahau tsalle awurin suna rungume juna. "Ya Asad thank u, yaaayyyy, Ya Asad u are the best wallahi" ihunsu yatada Sharif dake bacci hakan yasa yasauko ganin kudi a hannunshi suna rawa suna nunamai yasa cikeda wasa yace "yanzu sabida ku yan bakin ciki ne Asad na rabon kudi shine bazaku tasoni nazo na amshi nawaba " dasauri Rahima tace "bayan kahanamu damuka maka magana" hararanta yayi yaje gaban Asad dake aikinshi yana kallon ragowan 4 raps na kudin yace "Ya Asad nima abani nawa"? Dan hararanshi Asad yayi saikuma kaman bashiba yakalli su Aneesa yace "abashi" atare sukace "nooo Ya Asad" wani irin biyo su dagudu Sharif yayi aiko suka kwasa dagudu suka fita daga dakin yace "shegu yan bakin cikin yara kawai" murmushi Asad yayi sosai yace "kasai musu waya" juyowa yayi yaharari Asad yace " marasa kunyan yaran nanne zasuci kudina, ashe zasu mutu bawaya, Tara kudin aure nake" tabe baki Asad yayi yace "says wanda baida girlfriend" hararanshi Sharif yayi yace "Malam ya isheka fa kaita daga harkata tunda dai kahanani kudi". wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 1️⃣8️⃣ Tashi Asad yayi ya rufe system din ya ijiye sanan ya kwashe ragowan kudinshi yawuce wanshi sama, baiwani dade ba yasauko cikin jallabiya sabida sallan magrib da aka kira sai baza kamshi yake bayin falo shima Sharif ya shiga ya dauro alwala sanan yafito suka fice tare zuwa masallaci. Ana Magrib suka shigo gidan, dinning direct sukayi, zama sukayi Ammi na fitowa, Sharif yace "Ammi ina yaran nan wai nisukema dariya" dan hararanshi Ammi tayi tace "toba dole suyimaka ba nan nan yaran nan suka rokeka kudi kahanasu, anyway suntafi wajen Hajiya, kasan jikan Hajiya tazo shine ita sukaje gani nace musu nai musu kawa age mate dinsu ce wai zasu cemata ta shirya suje shopping tareda ita gobe" tsaki Sharif yayi yace "Ammi bani abinci na naci nima naje naga jikan Hajiyan muga ko za'ayi ta gida ne, Ammi tanada kyau"? Hararanshi Ammi tayi tace "inkaje ka gano da idanunka" tai maganan tana bashi plate na biryani rice, karba yayi yafara ci sanan ta zubama Asad dake daddanna wayanshi kaman bashi awurin. Biryani ta zubamai sanan ta turamai gabanshi tace "ina kaje dazu Asad" dagokai yayi yakalleta spoon yadauka zai faracin abincin yace "naje nasha iska ne kawai Ammi" ture abincin Sharif yayi yamike yace "Ammi natafi" wanan karan dariya Ammi tayi tabishi da kallo fita yayi abinshi, tashi itama Ammi tayi tai sama bata wani dade ba tafito rikeda drawing book din Du'a samin shi tayi zaune inda tabarshi yanacin abinci, kujeran kusada shi taja tazauna sanan ta ijiyemai drawing book din agabanshi, Ammi yabi da kallo saikuma ya ijiye spoon din dayakecin abinci dashi yadauki drawing book din yabude yana dubawa, ahankali yakalli Ammi yace "Ammi who drew this"? murmushi Ammi tayi tace "zanen yayi kyau" dasauri yana kallon drawing din yace "this is classic, I mean the hands behind this drawings is a genius, Ammi wow, idan yanzu nabada wayan nan zanen akai bringing this shoe to life my company zai zama number show brand company in the whole Africa" murmushi sosai Ammi tayi tace "zaka bama mai zanen aiki kenan"? sai alokacin ya kalli Ammi yace "who drew it Ammi" ahankali Ammi tace "zan gayamaka, but my zanen is very dear to me nai alkawari zaka bama mai zanen aiki dudda batai makaranta ba" dasauri yace "Ammi u mean mace ce tai zanen!" gyadamai kai tayi tace "yes mace ce, but batai school ba sabida some matsaloli irin na rayuwa, but she's talented, inason kabata aiki sanan kabiyata tsakani ga Allah yanda kake biyan illustrators dinka" yatsine fuska yayi yace "Ammi kinsan qualifications din illustrators dina kuwa, how can I pay wacce bada da credentials haka is not possible ma" fizge drawing book din Ammi tayi tace "then forget it" dasauri yace "okay naji Ammi kawo" ya karbi drawing book din yana kara dubawa, Ammi tace "yanzu yaushe zata fara aiki" ahankali yace "gobe Monday, for now Sharif will handle everything dan sai next week zan koma" wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR Free page EPISODE 1️⃣ 9️⃣ Gyadamai kai Ammi tayi cikeda jin dadi tace "Allah maka albarka Asad dina" murmushi yayi yace "Ameen Ammi, but who is the girl"? kaman bazata fadamai ba tace "jikan Hajiya ce, she's 21" yatsine fuska yayi yace "Ammi ni all those children banson raini fa" hararanshi Ammi tayi tace "to Uncle Asad, ya za'ayi ma tamaka raini, jikan Hajiya ai she's just like ur sister su Mariya idan tayi badaidai ba ka gyaramata, kuma batada raini ko kadan that I know" yatsine fuska yayi irin baimasan maganan nan ahankali yace "Ammi I want coffee" tashi Ammi tayi tace "bari nahado ma tunda yaran nan duka sun gudu gidan Hajiya sun barni nikadai" kitchen tawuce tashiga.... Yau idan kaga bakin Du'a har kunne, har Rahima dake feeling tagirme su bazata iya zama friend din Du'a ba jitayi tanason Du'a sabida yarinyar akwai kyau dudda sun lura duk sun fita wayewa basu wani damuba kafin kice me cika falon Hajiya sukayi da hayaniya, suka tasa Hajiya agaba sai tabama Du'a itama kudin shopping gobe duk suka tafi tare, itama 200k tadauko tabata daman tanason takai yarinyar shopping but bata sami lokaci ba waya ma tace "gobe idan zata dawo zata taho mata da waya" duk suna cikin uban hanayinan Sharif yay sallama, dasauri Rahima tace "kinga Du'a we have two brothers, wicked and harsh, yanzu zakiga weekend one din shike mana murmushi da wasa amman shine ba'acin kwandalan shi" Hajiya dake kallonsu tace "Au haka kikace Sharif shigo kaji yanda kannenka kebata maka suna" turo kofan yayi yashigo hakan yasa Du'a itama tadaga kanta dantaga wanda ake batawa, wani kyakkyawan gayene dogo mai tsayi gashinan fari fat kaman su Rahima, tana ganinshi taga kamanninshi da Rahima da Mariya, baida kiba ko kadan, sai uban kyau ga sajenshi baki sidik dasuke nan akwance, gashin baida tarin gashi irin na Asad amman akwai gashi kadan da lowcut yakeyi ko kadan bata ganeshi ba hakan yasa kawai ta tsaya tana kallonshi daga inda take zaune kusada Hajiya dasu Rahima. Dauke kai yayi daga kallon Du'a ganin kannenshi da kowa na wajen yace "Hajiya yanzu har gidanki suka tattaro sukazo suna gulmana yaran nan, aiko wlh zan baku kashi" yay maganan yana dunfaro su, ihu sukayi duk suka tashi suka kankame Hajiya Du'a ko sai dariya dasauri Hajiya tace "jama'a na shiga uku, wani yamikomin wayata yaga wlh Ammin ku zan kira tazo ta kwashi yaranta kutafi gida tunda neman kasheni kuke kai kuma wlh bazaka taba yaran nan agidan nan na ko kazo kazauna kokuma kawice katafi idan mugunta kazo yi nagayamaka kukuma ku dagani" Da sauri suka dagata shikuma yazo gefenta yazauna kusa da ita yay folding hannu yace "Hajiya jikanki batada kunya ita batasan yayanta yazo tagaidani ba wlh idan tace zata biyema marasa kunyan yaran nan nida ita bazamu shirya ba" yay maganan yana hararan Du'a, sosai Du'a ke murmushi ganin yanda Sharif keda ban dariya, ahankali cikin yar muryanta tace "Ya Sharif ina yini" hararanta yayi yace "lpy lau" Mariya dake gefenta tace "Ya Sharif kaga harda ita zamuje shopping din gobe tunda Ya Asad yabamu namu kai kabata nata ai itama kanwarka ne yanzu" dasauri Hajiya tace "ohh ni yasu Mari ke Mariya yaushe kika dawo scammer eh, Sharif yaran nan damfaran ka zasuyi ba yanzun nan nabama Du'a nata 200k dinba" dan sosakai Sharif yayi yace "Hajiya ni bansan ko yaran nan basuso nai aure bane, kudin aure fa nake tarawa" saikuma ya kalli Du'a yace "nasan sun riga sunce miki banda kirki I will prove them wrong, kinga ban shigo da kudi ba, but zanbama Mari gobe tabaki okay" gyadamai kai tayi tana kallonshi irin kaman bata yarda ba dinan dan ita Grandma tariga tabata kudin ta, kaman Hajiya ta lurada hakan ne yasa tace "baki cema Yayanki kingode ba" murmushi tayi ahankali tace "nagode Ya Sharif" nan fa dakin ya kachame da hira, shi Sharif baida girman kai yana shiga kannenshi yayi hira dasu sosai iyayensu dasuka rasu yasa yafara haka dan he is all dasuke dashi couple with the fact Asad baida wasa, saisa yake hira dasu yasasu dariya yasasu bakin ciki komi ba, daga karshema zamewa Du'a tayi tai bacci shoulder ta nakan jikin Rahima, sai wuraren 11 Sharif ya tarkatasu sukama Hajiya sallama suka tafi kaman karsu tafi, itakuma ta tada Du'a tawuce taje ta kwanta. Flat dinsu ya shiga yana maida kofa yarufe sanan yashigo ciki Asad yagani zaune afalo yana kallon wani horror movie a smart TV dake falonsu, tsaki Sharif yayi danya tsani horror movie zama yayi yace "kafara kallon film din aljannun nan naka ko" dagamai gira daya Asad yayi sanan yadauki drawing book din da Ammi tabashi ya jefama Sharif din, dasauri ya chapke yace "what is this" yay maganan yana budewa, ganin wasu hadaddun zanen takalma yasa yamike tsaye yacigaba da kallon su one by one. "woooooo Asad who drew this??? Wow Wow, waye yay zanen nan eh, we need this talent a company mu wlh, who drew this Asad" dan batarai yayi yace "Ammi takawomin wai I should hire wacce tai zanen a company mu" dasauri Sharif yace "of course Asad you should hire this talent karfi all those competing companies su gano mai zanen su rigaka hiring nashi, but waye mai zanen a ina Ammi tasamo maka" tabe baki yayi yace "tace wai jikan Ammi ce mai zanen, she's a small girl 21, kuma karatun ta a JSS2 ta tsaya due to some reasons best known to them, how can someone dabaida qualification zaimin aiki eh" dasauri Sharif yace "in this case don't look at qualification look at the talent, Asad ko bature illustrator dinka baitaba zana takalma masu kalan kyau dinan ba, this is masterpiece wlh, mukai takalman nan trust me all celebrities across the globe will be rocking ur brand, yarinyar nan tun wuri without second thought kadauketa" yatsine fuska yayi yace "Ammi tariga tasa nadauketa gobe zata fara aiki" dasauri Sharif yace "gobe" dan yasan gobe zasuje shopping, gyadamai kai Asad yayi yace "yes, inaso you should handle everything, interview her kasata a office na illustrator din let her get to work, guide her, before nagama this TV program in yaso once am back sai afara work on production" gyadamai kai Sharif yayi yace "okay Asad, bari naje na kwanta, kaine night owl" yay maganan yana stairs yana murmushi da gangan yaki fadamai wacece jikan Ammi yanaso yaga reaction dinshi ranan dazaiga wacce yace to daga rijiya ce jikan Hajiya ita yabama aiki. Wuraren 5:30 Hajiya tashigo dakinta, tadata tayi ahankali tabude idanunta tashi tayi ahankali tazauna Hajiya dake kallonta tace "guess what" bude idanunta tayi tarr tana kallon Hajiya, murmushi Hajiya tayi tace "kinsami aikin" wani irin murmushi tayi tawashe fararen hakoranta, Hajiya tace "amma ance yau zaki fara aiki, danhaka tashi kiyi salla kiyi wanka ki shirya yarinya na is now a working class young lady, my lucky jika" murmushi sosai tayi ahankali cikin muryan baccinta tace "Grandma shopping dinmu dasu Rahima fa" murmushi tayi tashafa gefen fuskanta tace "don't worry about that karfe 4 zaki tashi daga office idan kindawo sai kuje, yanzu tashi kije kiyi salla" gyadamata kai tayi ta tashi dasauri tai bayi alwala tayi tafito tai salla saida tai karatun Al Qur'ani tai addu'a Allah ya sanyama aikinta albarka sannan takoma bayi tayo wanka tafito mata shafa ta shirya cikin riga da skirt na atampa sanan tafito falo, tunda take saukowa Hajiya ke kallonta ganin yanda mahaukacin shape dinta yafito akayan yasa taji bata natsu ba, ko aikin ma data bari tayi sabida tasan Ammi da yaranta ne tasan yanda sukeda natsuwa kuma tasan zasu sa ido akan Du'a, saisa ta natsu da bata bartaba, sanan kuma tanason yarinyar takara girma tai wayau tasan ya rayuwa take outside home, kujeran dinning Hajiya taja mata hakan yasa ta zauna tace "grandma cikina namin wani iri idan natuna zani aiki" dan dariya Hajiya tayi tana zuba mata tea da Irish tace "kina feeling butterflies a ciki, it's normal, yanzu ci abinci karki latti fa, 8 ake zuwa aiki" dasauri tashiga cin bata wani ci sosai ba dan bata iyacin abinci sanan ta tashi, Hajiya tace "anya bazan sayo miki Vitamin B complex ba kuwa Du'a baki iyacin abinci, oya tashi muje sama kiga" tashi tayi sukai sama, dakinta suka shiga Hajiya tabude wardrobe dinta, wani sabon abaya taciro mata black mai mahaukacin kyau ta ijiye kan gado tace "inaso ki zama very wise girl, kinga kalan jikin da Allah yabaki dan haka bazaki dinga saka atampa haka kina zuwa aiki ba, zan karo miki hadaddun abaya masu kyau su zaki dinga sawa kina zuwa office okay, inaso idan kikaje ki natsu ba ruwanki da gulma ko surutun office respect ur senior idan kikai laifi aka miki fada take ur correction, karkiga sabida kinga Sharif ko Asad sabida kin sansu suna kaman matsayin yarana ne kidinga musu magana anyhow ko rashin kunya no, a office is strictly work and formal communication okay, ki natsu kafin ki zauna akan kujeran aikin ki da za'a baki kiyi addu'a, kullum idan kika shiga office dinki kafin kifara aiki kiyi addu'a hakan zaisa kidinga samin cigaba Allah na Buda miki, ki zama mace mai kamunkai, abinda yasa nama barki kiyi aiki sabida inaso ki sami experience ne kisan menene rayuwa dan bakisan komi kan rayuwa ba Du'a, be very smart okay, karki damu yau zan sau miki wata" gyadama Hajiya kai tayi tace "thank u Grandma" ajiye mata kayan tayi tace "oya shirya nima bari naje na shirya zan shiga office yau saina saukeki a company ku" wucewa tayi tafice, shiryawa tayi cikin doguwan rigan ita kanta saida ta kallo kanta saboda yanda tai wani kalan kyau, parking kalabanta tayi sanan tazauna kan kujeran tadau gyalen abayan tana kokarin rolling bata iyaba aka turo dakin aka shigo, Hajiya ce ta shirya cikin ubansun gown din lace rikeda waya tamikama Du'a tace "ga Mamin Ki" karba tayi takai kunnenta ahankali tace "ina kwana Mami" ajiyan zuciya taji Mamin ta tasauke tace "Du'a ya kike" murya chan kasa tace "lpy lau" murmushi Mami tayi tace "ance kinsami aiki Allah ya sanya alheri ki kulada kanki kinji" murya chan kasa tace "to" "OK bye" bye tace Mami ta katse wayan karban wayan Hajiya tayi tace "bani gyalen kiga namiki rolling" rolling Hajiya tamata tsaf, saita juya tana kallon gaban mirror hannu tasa tadauko wani pink janbaki da kwallin saka mata kwallin tayi sanan ta shafa mata Jan bakin kadan daya saje da lips dinta, kafin tadau turaruka ta fesa mata sanan tadauko wata jaka tace "idan mace zata fita most especially office haka makesure kinada pad kwata daya aciki incase of period yazo miki, sai wipes, sai lip balm, sai dan karamin turare haka dayar hoda ko madubi, pen da dankaramin jotter haka" tai maganan tana daukan komi tana samata ajakan sanan tabata jakan, karba tayi tana murmushi Hajiya tawuce tafita tace "sa takalmi ki sako" takalmi tasaka sanan tajuya takalli kanta a mirror wlh kaganta bazaka iya tantanceta da balarabiyaba tai wani irin kyau akayan, hakanan saitaga tama kanta girma tadawo wata babba kaman yar mai kudi jin Grandma ta kwalama ta kira yasa tajuya da gudu tafice. don magana dani M Shakur chat me up by clicking on this link wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR Free page EPISODE 2️⃣0️⃣ Razika da Shemau tagani a falo tsaye duk suna kallonta suna murmushi sabida tsabagen yanda tai kyau, sake washe musu baki tayi tace "natafi office" kwashe wa sa dariya sukayi sukace "adawo lpy Du'a, Allah yabada sa'a" Ameen ta amsa sanan tawuce tafita waje tana musu bye, tsakar gida tayi tana tafiya ahankali ita kanta Hajiya tsayawa tayi tana kallon Du'a to some extend bata wani cika blaming Kaka ba data dage cewa Du'a ba jikan ta bane dan wlh Du'a bata da banbanci da balarabiya ga kyau ga diri ance mutum tara yake baicika goma ba Du'a tamafi ashirin, fararen kafafunta Hajiya tabi da kallo dake kara haske bakin abayan data saka karasowa wajen tayi tace "muje grandma" murmushi tamata ta rungumo kafadan ta tace "kinyi kyau jikalle, yau kukaje shopping ki zabo takalma masu kyau da hills ba chan chan ba kinji, good shoes takes a woman to good places, takalman Du'a dina should be epic kaman cendarella koba hakaba" "hakane Grandma" tai maganan tana shiga mad jeep din Grandma, Grandma ma tashiga driver ta yajasu, hira Hajiya keta mata ganin she's a bit nervous daurewa kawai take wayaga sabon shiga, cikin wani ubansu glass building taga sun shiga mai tsawo wanda daga gani kasan akwai elevator dan sabida yanayin tsayinshi sunan company EPIC & COs LTD, parking direban Grandma yayi takalleta ganin yanda take kalle kalle tace "this is company dazaki dinga aiki aciki wuce kitafi" kallon Hajiya tayi idanunta sukai zuru zuru kaman zatai kuka tace "Grandma mezance" dariyan da Grandmaa keji ta hadiye tace "just go this is beginning of new phase, anriga an baki aikin so amsan da zuwanki idan kikaje akwai receptionist awajen ki gayamata sunanki she will tell u what to do, come here" Hajiya tama goshinta peck tace "Allah bada sa'a don't forget abubuwan dana fadamiki" gyadamata kai tayi gabanta nafaduwa sanan tabude kofan ta fita, direban grandma yajata suka wuce suka tafi suka barta tsaye awajen, haduwan ginin kadai yasa taji she's having change of mind ita daketa murna zatai aiki ita ko kadan batai picturing something like this ba irin wanan big organization dinne Ammi zata saman mata aiki ba, takai kusan 5min tsaye awajen sanan ta dage tafara tafiya towards the entrance door da kofan yay kala da kofan bank, taga yanda mutanen dake wucewa ke shiga hakan yasa itama taje, security dake wajen ne dake bada hand sanitizer ne yabita da kallo sanan yace "ur hand Miss" muka hannunta tayi aka zuba mata ta shafa yace "u can go in" shiga kofan tayi nan kawai taga glass yarufe ta ihu tayi tashiga buga glass din. "wayyooo Allah na innailaihi Grandm......" bata karasa kiranta ba taga kofan ya budu ga mutane dayawa awajen kowa na harkan gabanshi bama a lurada ita ba yasa tashare hawayen daya zubomata da sauri tashiga tana kalle kalle still ganin desk da counter da aka rubuta reception yasa tai wajen, wata hadaddiyar chic ce awajen kafinma Du'a ta isa wajen yarinyar ke kallon Du'a kaman zata hadiyeta tace "how can I help u Miss" ahankali Du'a tace "my name is Du'a Muhammad" dasauri receptionist din tace "the new illustrator, please come with me Miss Du'a" Receptionist din ta tashi tai hanyar elevator Du'a biyeda ita suka shiga, 4th floor ta danna da elevator yafara tafiya runtse ido tayi danji tayi hanjinta na neman fitowa, wani complete new section tagansu aciki saiga wata secretary dake zaune gaban system ga kujeru zaman mutane awajen, nunama Du'a kujera tayi tace "have a sir Miss Du'a" sanan takalli secretary dake kallon Du'a tace "she's the new illustrator, u take it from here" gyadamata kai tayi tawuce itakuma Du'a ta zauna tana kallon office din dake gabanta dakenan arufe jikin kofan anrubuta M.D Mr Sharif Alameen Kitse, takai kusan 1hr azaune awajen sanan aka bude kofan wasu manyan baki dake sanye da suit turawa suka fito tareda Sharif dake sanye da suit yayi wani irin kyau, binta yayi da kallo sai baice komiba yawuce yataka bakin har zuwa wajen elevator sanan suka shiga yadawo ya tsaya gaban secretary din cikeda fushi yace "tun yaushe Miss Du'a ke zaune anan Miss Amal"? dasauri matan tace "about an hour ago" "and u couldn't take her to her office" yafadi ranshi abace, tashi Miss Amal tayi tace "sorry sir I thought zaka fara ganinta ne tukunna saisa na bartaka sallami baki tukunna" cikeda takai takaici yawuce gaban Du'a yace "I apologize for that Miss Du'a, shall we" tashi tayi tana gyadamai kai yabude office dinshi yashiga tana biyeda shi sai kallon office din take yanda office din yahadu kujera yanuna mata ta zauna sanan shima yawuce ya zauna yakalleta da murmushi a fuskanshi yace "you want coffee kona kaiki cafeteria kici abinci"? Gizgizamai kai tayi ahankali cikin muryan nan nata mai bala'in dadi tace "I had breakfast thank you" cikeda gamsuwa yana kallonta yace "it's fine, anyway welcome to EPIC & COs LTD, company ne that is into creating and inventing all kind of shoes dakika sani da different materials, starting from animal skins har zuwa leather shoes, munada lots of investors da abubuwa da yawa which I believe since kina nan yanzu u will understand everything, Today is all about introduction babu abinda zakiyi gobe ne zaki fara aiki officially, that aside. My name is Sharif Al Ameen Kitse, nine MD wato managing director of this company, sorry bazaki sami daman ganin CEO dinmu ba dan he's officially on leave sai next week zai dawo, I will give u a tour around the company har zuwa warehouse dinmu dake kasa inda ake hada takalman da ire irenki ke zana mana, zan kaiki HR department zaki miki small abu za'a dauki hotonshi da some biometric dan za'a miki ID card na aiki, we have mosque we have church, rest room cafeteria duk acikin nan, and if u are having any difficulty with anything feel free to give me a call okay I'm ur brother banda haka Hajiya tace nakulan mata da jikan ta inba hakaba saitaci kaniyana" yay maganan cikeda wasa yana kallonta dan murmushi tayi itama dan sosai yanada kirki, ahankali yace "are you ready for ur tour ko kina bukatan wani abu, water juice ko cingum ko sweet kinsan mata da kwadayi remember I have sister nasanku, nabaki sweet"? yay maganan yana jawo wata yar locker shi yanuna mata, uban sweet ne na chocolate da sauransu aciki yana kallonta, kasa cemishi a'a tayi ahankali yasa ahankali tace "eh" ciko chocolate da sweet yayi a hannunshi yamika mata hannu tasa takarba ahankali tace "thank you" jakanta tabude ta zuba sanan tadauki daya tabude tasa abaki, murmushi yamata yace "let's go" gyadamai kai tayi tabishi suka fito tana biyedashi suka shiga elevator, ya danna 5th floor yace "let's start with 5th floor nanne floor na Oganmu duka, CEO anan kuma office din illustrator company yake dan haka anan office dinki yake" jin shiru yasa yajuyo yakalleta gani yayi ta kankame idanunta lips dinta na motsi, dan murmushi yayi yace "scared of elevator"? Gyadamai kai tayi ahankali daidai kofan nabudewa yafice ahankali tafito itama idanunta har sunyi ja sabida tsoro, tazaci 4th floor nada kyau dasukazo fifth floor dinnan saitaga wane 4th, ga mutane sai aikinsu suke sai gaida Sharif ake ana bin Du'a da kallo dashi kanshi Sharif saida ya lura, gaban wani office yaje dake kusada CEO dan tazaran ba yawa taga an rubuta illustration, bude kofan yay ya shiga yajuyo ya kalleta yace "come in" shigowa tayi tana bin office din dakallo table ne hadadden gaske da laptop ke kai ga kujera dake juyawa, ga dogon couch, sai frames a bango na zanen takalma masu kyau, sa shelf dawasu irin hadadden drawing book dabata taba ganinsu arayuwanta ba suke ganin su take kallo yasa, Sharif yadauko daya yace "anan zaki dinga zanen it's digital drawing book, kome kike zanawa is connection to this MacBook" yanuna mata laptop din dake kan kujeranta, yace "we can't wait for xanenki, you can keep ur bag dan nanne official office dinki" gyadamai kai tayi ahankali ta ijiye jakanta kan table sanan yakalleta yace "mucigaba kokin gaji" murmushi tamai ahankali tace "mucigaba" fita yayi tabishi wanan karan saitaga baibida ita elevator ba sun dauki stairs hakan bakaramin dadi yamata ba harsaida ya lura dansai murmushi takemai, suka tafi kowani floor yana nuna mata komi, sukaje Cafeteria company babban gaske all employees dinsu are entitle to lunch kaje za'a baka free lunch, dasafe kuma kowa is entitle to either coffee ko lip tea saisa kowa nan yake fara tsayawa dasafe ya karbi tea sanan kowa yawuce office, yakaita mosque incase tanaso tazo tai salla, yakaita warehouse, yakaita HR yana tsaye akai taking biometrics dinta aka mata passports saida tagama komi sanan suka taho abin har mamaki yadinga basu wanan tour din dayake bata ba aikinshi bane, sake komar da ita Cafeteria yayi yakalleta yace "tea or coffee"? murmushi tayi kaman mai tsoro tace "tea" sawa yayi aka hada tea a coffee aka kawo musu a disposable cup mai marfi yabata nata yana rikeda nah I yace "muje" sakebin bene yayi da ita suka tafi har 5th floor, office dinta yakaita yace "now sit round relax do anything dakikeso, if u want anything just dial my number awanan landline Din" yanuna mata telephone din wajen yace "dial 444 zaiyi connecting naki to me" gyadamai kai tayi, waving mata hannu yayi yace "bye" ahankali tace "bye" harya wuce saikuma yaleko yace "drink our tea kiji da dadi kafin yahuce" gyadamai kai tasake yi tana murmushi, wucewa yayi yatafi abinshi, zama tayi kan kujeran ta da tuntuni yake shigan mata idanu tahau wasa akai tana juye juye saikuma tamika hannu tadauki cup din tashiga shan tea aiko dadi hakan yasa tacigaba dasha tana murmushi ita kadai. wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR free page EPISODE 2️⃣1️⃣ Sosai takebin office din da kallo kaman wacce bata taba ganin office ba arayuwanta, ga katoton TV dake makale a bangon office din, gawani camera Ata sama amakalle shima dabata san koname ba, ahaka tana zaune ita kadai har lokacin azahar tayi, knocking office dinta akayi saikuma aka budo kofan, Sharif ne murmushi lullube kan fuskanshi yana kallonta batare daya shigo cikin office dinba, dan murmushi tasakinmai itama dan wani irin kunyanshi takeji ganin yanada kirki sosai, ahankali yace "is time for zuhur u wanna join me?" Gyadamai kai tayi da sauri dan tuntuni takejin fitsari dama amman kunyan tafita ita kadai takeji taje, tashi tayi ahankali tafito duk yana kallon ta sanan taja kofan office din suka wuce tare har mosque yanuna mata side din mata ta tafi, wucewa tayi bayinsu sai kallonta matan dake wajen suke itadai babu wanda take cema uppan besides ma kanta akasa dan kunyan yanda suke kallonta takeji, fitsari tayi tayo alwala sanan tashigo masallacin ganin cupboard dake cike da hijabai yasa tadauki hijabi tasaka tai salla abinta, tana idarwa ta zauna tana kokarin rolling gyalenta babu yanda batayiba takasa hakan yasa takama gyalen ta wajen wuyanta gamgam tamike tafito, jigine da bango masallacin taga Sharif yay folding hannunshi akirji da alamu ita yake jira, ganinta yasa ya yunkura yataho inda take yana kallonta yace "maiya sami gyalen"? Ahankali tace "ban iya yanda Grandma tamini ba" Dan murmushi yayi yace "then u have to learn dagayau, let's go have lunch" yay maganan yana hawa stairs yay hanyar canteen dinsu tana biyeda shi, shiga sukayi ga few employees dinsu dake wajen suna cin abinci cikeda girmamawa suka shiga gaidashi amsasu yayi batare daya kallesu ba sanan yaja kujera yanuna mata alamun ta zauna zama tayi ahankali tana kallonshi ganin yanda yake wani kulada ita kaman yar kanwarshi, shima zama yayi yakalli yarinyar datazo cikeda girmamawa tace "mezan kawo muku sir" batare daya kalleta ba yace "I want pasta da salad, mezakici Du'a" yay maganan ahankali yana kallonta, kallon yarinyar tayi sanan tace "jallof rice" juyawa yarinyar tayi ta tafi itakuma tasauke kanta kasa tana wasa da yatsunta Sharif sai kallonta yake kaman yamata magana saikuma yay shiru shima ahaka har aka kawo musu abincin, cin abincin shi yafara hakan yasa yace "bazaki ci ba" Dan dagokai tayi ta kalleshi ahankali tadau spoon tafara cin abincin, bini bini yake satan kallonta, ta bala'in yima kyau, komi nata daban ne, harya gamacin abincin shi batai rabin nata ba hakan yasa yacigaba da jiranta, kadan takara akai ta ture hakan yasa yace "u okay" gyadamai kai tayi tasha ruwa sanan ta tashi alamun su tafi tafiya sukayi har office yasake rakata sanan yawuce nashi office din, wuraren 4 tana zaune a office dinta telephone din wajen yahau kara dasauri ta dauka, muryan wani security taji. "Miss Du'a your driver is here to pick u up" dawani irin sauri ta tashi tana hada yan tarkacenta ajaka ta kosa ta ganta agida sanan tafito tana tafiya ahankali tasauka kasa zatai hanyar kofa taji magana a bayanta. "so you're living without saying goodbye" dawani irin sauri tajuyo ganin Sharif ne yana rikeda waya a kunnenshi da alamun ma waya yake but still saida yamata magana yasa adan kunyace tamai waving hannunta tace "bye" gyadamata kai yayi yacigaba da magana. "yes I can hear u Asad" waje tafita ta shiga motan Grandma dinta driver yatafi da ita, Allah Allah take takai gida, suna kaiwa gida tafito daga motan dasauri harda dan gudun ta tai falonsu tana budewa taga su Rahima Mariya da Aneesa duk sunci gayu sosai suna zaune afalon Hajiya atare sukace. "surprise" suka tashi suna rungumeta, wani irin murmushi tayi ta kallesu tace "yaushe kukazo sorry" dasauri Aneesa tace "bakomi Hajiya da Ammi daman sun gayamana kinji aiki, jekiyi wanka kizo kici abinci mutafi" gyadama musu kai tayi takalli Grandma dinta dake zaune tana kallonsu tana murmushi, wajenta taje ahankali tace "Grandma ina yini" fuskanta tashafa tace "Du'a dina sannu da zuwa, yi sauri kije ki shirya kunga tuntuni su Aneesa ke jiranki" wucewa sama tayi da saurinta dakinta ta shiga, wanka tayo tafito, tunawa da abinda Grandma tafadi mata yasa tasake dauko wata gown wanan is simple dan ba designers bane irin na dazu data sakaba milk color, saka shi tayi sanan tadauki mayafinshi ta feffesa turare tafito kasa, duk juyowa sukayi suna kallonta Aneesa tace "mena rike dankwali a hannu kiyafa mana" karasowa falon tayi tace "ban iya bane grandma zatamin" tabama grandma dan kwalin, dasauri Mari tace "Hajiya bari mu mata sabida ta iya" tana maganan ta karbi veil din daga hannun Hajiya sanan ta wani irin yafama Du'a akai gaban kanta daya cika da kwantaccen gashi yawani fito, Rahima tace "wow wlh kinyi kyau Du'a mutafi to, Aneesa ina kudinta da Ya Sharif yace mubata" dasauri Aneesa tashiga bude handbag dinta wani kudi taciro a envelope sanan tamikama Du'a din tace "ga kudinki, tundazu dasafe kafin yatafi office yabamu mubaki" dasauri Du'a takalli Hajiya danharga Allah batasan mezatayi ba, murmushi Hajiya tayi tace "karba Allah ne ya ciyar dake kafin aci kudin Sharif saidai idan Allah ya tsaga da rabonki ne" kwashewa da dariya yaran dukansu sukayi sukace "wlh kuwa Hajiya Ya Sharif kare bayacin kashinshi, karba muje" Ahankali tasa hannu takarba tace "thank u" sanan tasa ajaka, sallama sukama Hajiya sukai tafi direba ya kwashe su, sosai sukema Du'a hira a mota ita abin mamaki yake bata yanda suke sonta daga ganinta jiya dan har labarin samarin su suke bata, Aneesa data zauna agaban mota ne tajuyo ta leko takalli Du'a tace "ke baki bamu labarin saurayinki ba" Dan zaro idanu tayi tanuna kanta tace "ni"? dasauri Mariya dake gefenta tadan bugi kafadanta tace "common on don't be shy, tell us about the lucky guy" dan murmushi tayi saikuma tadauke kai dan tambayan tabata kunya ahankali tace "ni banda saurayi ko daya wlh" wani irin bude baki sukayi suna kallonta sabida mamaki, Rahima dake gefen Mariya tace "Du'a wasa kike ko" girgixa kai tayi tace "wlh ba wasa nake ba" shiru duk sukayi yanda yarinyar nan keda kyau ace bata da saurayi basu wani karyata ta sosai ba sabida sunga ko wayama batada shi, share maganan sukayi suka shiga wata hiran har sukakai mango dazasu, nan Du'a taga yanda ake shopping ita bama tasan mezata dauka ba hakan yasa kome suka dauka itama saisun daukan mata anata cart din, tundaga kan Bra da tuni suka gwadata suka shiga zakulo mata sizes dinta zuwa pants, pads kayan makeup, duk suna tura cart dinsu kowa na diban abinda akeso TV super market din dake makale asama na aiki Channels television news inda ake program REINVENTING THE NIGERIAN YOUTH.... Suna tsaye bangaren English wears Rahima ta amshi tape tana kokarin ana waist din Du'a dan asan size din jeans dinta itama ta dauka kaman daga sama wani kyakkyawan eloquent voice yadaki dodon kunnuwan Du'a da hakanan taji kaman tasan muryan, dawani irin sauri tadaga kanta sama takalli TV, chak ta tsaya ko motsi kirki tasaka, idanunta ne suka sauka kan fuskan da kusan kullum saitaga fuskan, wanda yacetota daga rijiya, yana sanye cikin wasu classic suit dark blue, ga necktie awuyanshi, yana zaune kan wata hadaddiyar kujera yayi crossing legs dinshi in a stylish way, yadaura hannunshi biyu kan cinyanshi wrist dinshi na daure da agogon Rolex, idanunshi fari kalll wanan karan babu bakin glasses akan su, lips dinshi sunyi wani masifaffen pink kaman ya shafa janbaki pin akai, gashin kanshi dake da yawa sunyi wani kalan extraordinary coils, yana magana da english da accent dinshi na bristish, kaman acikin mafarki taji ana Du'a, Du'a, Du'a, tabatan da akayi yasa tai firgigit tafarka ta kallesu da sauri dan sai alokacin ma tasan ashe tayi nizan tunani ne, neck dinta Rahima takai hannunta ta taba tace "baki da lafiya ne? Tunanin me kike haka kin tsare TV da ido eh harmun gama siyan kaya" binsu tayida kallo ganin yanda suke kallonta kaman sun damu yasa takakalo murmushi tace "tunanin abubuwan dazan saya fa nake" murmushi dukansu suka mata, Rahima tace "mungama da wanan shop din next stop is abaya store, mutafi mubiya mufice yamma nayi" gyadamusu kai tayi tabisu zuwa wajen cashier tana kara waigowa tana satan kallon TV da Asad har lokacin ke magana, kowa kudinshi yabiya sanan aka musu parking kayan a leda sanan suka wuce suka fita still saida takara waigowa takalli TV, sanan suka fice, ranan basu suka dawo gida ba sai 8 nadare kasa bude kayan tayi salla ta lallaba tayi sai bacci tashinta grandma tayi saida ta tasa ta agaba taci abinci sanan tabarta takara komawa bacci da tagaji bata saba fita ko wahala hakaba, all abinda tasani is wanka kwanciya da cin abinci shikenan saisa tai bacci awahale. DAN MAGANA DANI M SHAKUR CHAT ME UP BY CLICKING ON THIS LINK wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 2️⃣2️⃣ Kaman an tsikareta wuraren 4 na asuba tafarka da kanta batare da an tadataba, TV dake bangon dakinta ta tsaya chak tana kallo kaman mai tunanin wani abu, dasauri ta yaye bargon data lulluba dashi tasauka daga kan gadon, kunna switch din bangon tayi nan TV da decoder na DSTV duk suka kunna komawa tayi tazauna kan gadon tana sosa idanunta dake cikeda bacci, tadauki remote tashiga neman channels television news, da kyar ta iya ganoshi ta saka da sauri tana gyara zama kaman akwai abinda take shiri ta kalla, ganin ba abinda take nema sukeyi ba yasa tashiga wasu channels din tana skipping amman duka bataci karo da abinda take nema ba yarda remote din tayi akan gado sanan ta tashi tashiga bayi tai duk abinda zatayi sanan tafito dadduma ta shimfida tai nafila sanan tadauki Al Qur'ani tashiga karantawa har aka tada salla hakan yasa tarufe tai salla tana idar wa tai azkar ta tashi sanan tawuce tafito ko kadan batajin dadi, gaban dakin Hajiya tayi knocking tayi sanan tabude kofan ta shiga kan dadduma taga Hajiya zaune tana lazimi, ahankali tace "ina kwana Grandma" murmushi tamata tace "Du'a jiya angaji anyi bacci dawuri, tashi ga wayanki chan na samiki a chaji ina ganinma yacika" dasauri takalli inda ake nuna mata hadadden waya ne a bango dawani irin sauri tafada Jikin Hajiya batasan meyafaru ba kawai saita saki kuka sosai tunda tazo gidan nan she has been so happy, babu mai takura mata ko matsa mata ko kyaranta, ba'a taba bata matarai ba, ba'a hanata zuwa ko'ina, she's truly happy, jin yanda take kuka yasa grandma ta kankameta itama ahankali tace "I promise you Du'a inhar inada rai adoron kasan nan u will never be sad again, wlh wanan karan ko uban waye kulleshi zanyi akanki, abinda kika going through agidan mahaifinki u will never go through that again kinji, kina tare dani anan har aurenki, I will take care of you, malamin islamiyya da boko ma na saman miki zai dinga zuwa Saturday da Sunday, u will excel kinji, forget komi dayasameki abaya kaddara ce, kyaune Allah yabaki amman hakan bazaisa ki karake rayuwanki a kulle adaki ba dan haka u will learn how to live with ur beauty kinji Du'a dina" gyadamata kai tayi ajikinta ahankali, dagota Grandma tayi takai hannunta kan fuskanta tana share mata hawaye tace "ba'a kuka agidan Hajiya, now tashi kidauki wayanki kije falo ki kwaso kayan shopping dinki ki jera komi a inda yakamata adakinki, idan aikin yamiki yawa ki kira su Razika su tayaki" gyadamata kai tayi ta tashi daga kan jikinta wayan tawuce tadauka tana kallo, iPhone mai kyau 11 pro max Grandma dinta tasai mata ga Sim din MTN aciki, fita tayi daga dakin taje falo ta kwaso kayayyakinta tadawo dakinta, ta shiga jera kayayyakin, harda bags da shoes hadaddu, masu tudu da flat, ga kayan kwalliya, saida tagama tsaf sanan tashiga bayi tayo wanka tafito, shiryawa tayi cikin hadadden abaya again kaman yanda Hajiya tafadi mai ruwan kasa, tai rolling gyalen da kanta dan jiya sauka su Rahima suka koyanata a shagon abaya sunma sai mata pins na kama gyalen tasa pin din, sanan tadauki wayanta tasa a jaka tasaka wani takalmi baki mai dan tudu kadan dayama farin kafanta kyau sosai sanan tafito, a falo taga Hajiya zaune tana shan ruwan bunu kusada ita tazauna tace "grandma bazaki je office yauba" murmushi tamata tace "nariga nai retire, idan kinga naje office ko akwai wani important meeting ne, kokuma naje supervision, tashi kiyi break direba na jiranki zai dinga kaiki yana zuwa ya daukoki kullum, banda latti koni bana tolerating late coming dan tahaka ake discipline na employees, go and eat" tashi tayi tawuce yau tayi breakfast kadan saita shiga kitchen wani karamin roba tadauko mai marfi ta zuba pepper meat aciki duk Hajiya na kallonta sanan ta taho tasa ajaka tana murmushi ganin Hajiya na kallonta, dan hararanta tayi tace "da yanda kikecin nama haka kikecin abinci danaji dadi kura kawai" dariya tayi tarataya jakan a shoulder tace "Grandma Byeeee" Bye Du'a ayi addu'a, gyadamata kai tayi tafice Hajiya na kallonta tundaga kan kafafunta kafanta badai kyau ba ya ilahi, tana ganin zatamai fara sakata sa Safa, mota ta shiga direba yajata zuwa office. Yau tana shiga batai kauyencin datayi jiya awajen kofa ba, glass din na budewa ta shiga ciki, mutane sai kallonta suke maza da mata, saukar da kanta kasa tayi tana tafiya ahankali kafafunta na neman hardewa sabida yanda ake kallonta, dukfa sun tsayar da aikin dasuke kallonta ake, this is the first time data shiga waje kowa ya tsayarda abinda yakeyi yana kallonta, wani irin rawa jikinta yafara kafanta na hardewa daidai tazo stairs tahau kafanta yaturgude baya tayi zata fadi, jitayi antareta ta baya an daura hannaye biyu akan kafadunta murya chan kasa taji ance. "careful" dawani irin sauri tajuyo ta kalleshi, Sharif ne yana sanye cikin suit black yay wani irin kyau, hannayenshi dakekan shoulder dinta ya kalla sanan yajanye su ahankali murya chan kasa yace "sorry about that" sanan yajuya daga inda yake yakalli ma'aikatan su da ganinshi yasa kowa yafara aikin gabanshi kaman da gaske dan kwafa yayi sanan yajuya yakalleta yace "let's go kinada aiki yau" yay maganan yana gaba ahankali tabiyoshi abaya, Cafeteria dinsu yaje yakarbi cup biyu yajuyo na tea yabata sanan yarike na coffee sukai stairs yana tafiya yace "omg, at this points knees dina sun kusan cirewa kuma duk kece Du'a, mezan fadama future wife dina idan suka cire" dan murmushi kadan tayi tana binshi abaya batare datace komiba hakan yasa yajuyo yakalleta, boye murmushin tayi dan zaro idanu yayi cikeda wasa yace "did u just smile knees dina na aching" ahankali tace "sorry" juyawa yayi yacigaba da tafiya yace "zan gayama future wife dina it's one gurl called Du'a tasani nake bin stairs zuwa 5th floor fa sabida tana tsoron elevator" murmushi tasakeyi batace komiba har sukakai office dinta, shiga sukayi ta ijiye komi kan table ta tsaya agefe, juyowa yayi ya kalleta yace "me kikeyi abayana sit akan kujeran ki nabaki aikin ki natafi" gyadamai kai tayi tazo ta gabanshi tawuce tazauna kan kujeranta ahankali kaman mai tsoro, wani karamin mini pad yamika mata yace "the CEO sent this, yanaso kiyi zanensu next week idan yashigo aikinsu za'a fara, 5 design na hills, 5 na loafers, 5 different design na croc and unhooked sandals" ganin yanda take kallon pad din yasa yace "it's a whole lot of work ko, don't worry take ur time zaki iya kadan yau kiyi sauran gobe" gyadamai kai tayi ahankali hakan yasa yajuya yace "in that case bari natafi" haryakai kofa ta dago kanta ahankali tace "ummmm" juyowa yayida sauri yakalleta yace "da wani abu ne"? gizgiza mai kai tayi tace "thank you, su Rahima gave me the money, Allah amfana Ya Sharif" tunda take maganan harta gama yake kallonta, dauke kai yayi yace "you are welcome" sanan yawuce yafita daga office din. Ranan haka tawuce zane take a E-board dinan, bakaramin burgeshi zanenta Sharif sukayi ba, kafin 4 tagama gabaki daya ma dan she's so fast da zanen tawuce ta tafi direba yadauketa. Tana shiga gida tafito tawuce ciki, Razika da Shemau tagani zaune a falo suna kallo TV tabi da kallo ganin film suke kallo yasa tace "ina Grandma" Razika dake kallonta tace "tana sama kaman ta kwanta bata dade da shigowa ba" sama tayi ahankali tabude kofan dakin Hajiya ganinta kan gado tana bacci yasa tawuce dakinta, kaya tacire tawuce bathroom wanka tayo tafito daure da towel tayi gaban wardrobe wani simple short gown tadauka tasaka, jin anyi knocking kofar ta yasa tace "shigo" shigowa Razika tayi dauke da tray na abinci tace "abinci nahado miki nasan kin gaji" wani irin murmushi tayi Razika nada kirki karban tray tayi tace "nagode Razika" gyadamata kai tayi tawuce tafita zama tayi kan gadon ahankali rikeda tray din tana kallon sinasir dake cikin plate, ga lafiyayyen miyan taushe dayaji naman kan Rago, dago kanta tayi sai kawai tacire tray kan jikinta ta ijiye agefe tamike tsaye da sauri switch din TV ta kunna tadau remote takoma kan gado ta zauna, gama booting yayi hakan yasa ta kunna tashar Channels Television News, daidai an nuno wani daga cikin audience ya daga hannu, hoster tace "go ahead" mikewa tsaye yace "My name is Samuel Madina Chris, My question to Mr Asad Abdullahi Kitse is you see we all know you come from a wealthy home/family, so setting up a business starting a company can not be a problem for you cus ur family are buoyant enough to support you with startup capital, mu yanzu that come from not so financially strong family how can we source for start up capital dan bamu da yan uwan dazasu taimaka mana"? Nuno Asad akayi, yau yanacikin wani hadadden suit ash color dark ash da yamai bala'in kyau, yay crossing leg as usual, looking so elegant and classic, gashin kanshi sun kanannade suna wani irin kyalli, lips dinshi sunyi pink yirrrr....... Ahankali Du'a tawani irin sauke ijiyan zuciya idanunta kur akan TV akanshi gabanta nafaduwa dum dum dum....... Gyara zamanshi yayi yay adjusting mic din dake gabanshi wani dan karamin cute smile yasaki dako hakoranshi basu bayyana ba cikin husky melodious voice dinshi yace "I appreciate this question Mr Samuel you know why" yadanyi shiru kafin yadan ciki lebe kadan yace "sabida mutane dayawa nada wanan misconception din, suna tunanin all mutanen dasuke business are from wealthy homes, lemme tell you all something, mahaifina nada companies, yanada kudi, but kunsan 1naira na mahaifina kona family na banyi amfani dashi a business dina ba, I strive for my business with my hard earn money" wani irin tafi hall din yadauka hakan yasa yay shiru yana jiran sugama yace "akwai lots of organizations that ayanzu the youth can reach out to dan su sami kudi and establish business dinsu ko expanding business dinsu, CBN, SMEDAN, BOI, and so much more, listen business is not for the lazy ones dayay depending on his families, and is not for the ones that doesn't have the zeal to strive hard and hard and hard to achieve his goals, business is for people that doesn't believe in impossible, don't tell ur self is impossible to establish a business because my parents are poor I don't have any source of income..." wani irin tafi aka fara a hall din kowa na having goosebumps sabida yanda yake maganan yana penetrating a zukatan audience din, saida sukai dan shiru sanan yace "business na mutane ne that believe in their self, people that have vision and are ambitious, people that are vasitile and strong hearted, we'll ladies and gentlemen I think we've reached the end of today's program saikuma gobe, thank you" wani irin tafi aka fara a hall din kowa yamike tsaye anamai tafi shikuma yawuce yana tafiyan nan kaman zaki looking damn elegant, classic and sexy yawuce yafita daga hall din, tashi itama Du'a tayi ahankali tama rasa mezatayi kawai saita koma ta kwanta kan gadon ahankali tana kallon TV da har anfara another program. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR Free page EPISODE 2️⃣3️⃣ Lumshe ido kawai tayi looking so somehow da bazaka tabace ga asalin yanayin datake ciki ba, ahaka bacci yay awon gaba da ita saida Hajiya tashigo ne ta tadata taje tai salla sanan ta sata agaba aka kawo mata wani abincin aka tafi danada dan bataci ba sanan tabarta ta kwanta dan akwai baccin sosai a idanunta. ****** Ahaka tai good five days a company from Monday to Friday Sharif has always been there for her, yanada kirki mara misultuwa, he's very nice and generous kaman ba boss dinta ba at all, yamaida ta kaman wata sister dinshi hakan yasa itama tadaukeshi kaman wanta Ya Hamad, itadasu Rahima kuma kaman sunsan juna tuni suka koya mata watsapp suka sakata group dinsu na yammata inda ake hiran samari da heart break ita saidai ta karanta taita mamaki, kullum 4 nayi take fitowa driver Hajiya ya dauketa tana dawowa gida zata gudu dakinta tasaka channels television news but kodaa yaushe ending din program din Asad take samu wani zubinma bata samin takalla kafin takai gida an gama barin ma ranakun da holdup yakamasu, har kasan ranta she wish zata iya ganinshi tace mai thank u for saving life dinta dan ko kadan takasa manta da fuskanshi da idanunshi dasune tagani da kyau danhar kasan zuciyanta takasa mantasu. Yau Saturday su Rahima sunso sujata yawo Grandma tahanasu dan malamin ta zaizo, wuraren 10 malamin bayerabe yazo, Hijab tasaka har kasa tafito karatu yamata both na boko da islamiyya dan irin genius ustazan malaman nanne, karfe one suka gama yatafi, dakinta takoma ta kwanta yau kawai she's so happy koba komi tana gida zata kalli program dinan daga farko har karshe yau, salla ta tashi tayi jin ankira sanan takoma ta kwanta sai bacci, wuraren 3 Hajiya tashigo dakin tadata tayi. "ke Du'a oya tashi" bude ido tayi ahankali ganin Hajiya yasa ashagwabe ta daura kanta kan cinyarta murya chan kasa tace "Grandmaaa nagaji" smooth kumatunta Hajiya tashafa tai murmushi tace "oya tashi sonake ki shiga kitchen tareda su Razika kema kisoma iya girki, tuwon shinkafa zakuyi da miyan taushe sai farfesun kifi" ahankali tabude idanunta dahar sunyi dan ja sabida baccin datayi takalleta, tashi tayi zaune sanan tamike tsaye tace "grandma dakaina zanyi girkin ni kawai su nunamin yanda zan dinga yi" gyadamata kai Hajiya tayi tana murmushi tace "to gimbiya Du'a hakan za'ayi" wani kalan murmushi tayi cikeda murna tawuce tafita daga dakin dan tafi kowa so ta iya girki dan girki na burgeta, shiga kitchen sukayi aiko su Razika sun sha dariya dan targen tuwo bata iyaba haka suka dinga koyanata suna dariya gabaki daya ta manta da abinda takeso tayi, saida suka gama tuwon sanan ta kalli agogo dake manne abandon kitchen din, dawani irin gudu tafita daga dakin ta sama dakinta tashiga, TV kawai ta kunna dan decoder a kunne yake dama tana kan channels din, ganin angama program din yasa taji wani abu yatokare mata wuya, wata matace ta bayyana agaban TV tace "to jama'a ni karan kaina bakin cikin sanar daku nake cewa a yau ne wanan program din da gwamnatin Nigeria takawo muku sabida tallafawa Matasan kasa wanda wanan shahararen matashin nan dan kasuwan nan wato business Mr Asad Abdullahi Kitse ya gabatar muku yazo karshe, ku saurara kuji" matan tayi murmushi tace "channels television news tasami sakonni da dama kan shafukansu na sada zumunta da emails kan Mr Asad cewa mutane naso sugana dashi, toga wata sanarwa, gwamnatin Nigeria tashirya kyakkyawan liyafa wato dinner nagama wanan program din agobe karfe 4 na rana inda star dinku Mr Asad zai hallata, ana gayyatan marasa su fito duk kuzo dan Mr Asad zai sake bayarda jawabi wato speech awajen dazai taimakawa marasa wajen fara tasu sana'ar, za'ayi wanan taro ne ababban hall din transcop hotel, a huta lpy" daidai nan suka shiga talla kuma, zama tayi ahankali kan gado tai shiru, kwala mata kiran da akayi yasa ta tashi tafita daga dakin da sauri suka daura miya, suna gamawa ta debi nata tafito ta tafi dakin Grandma dinta dake waya hakan yasa tai zamanta tanacin tuwon. Gama wayan Hajiya tayi tace "iyye manyan mata anyi mana girki yau" washe baki tayi tace "grandma abincin nan dadi wlh sosai" hararanta Hajiya tayi tace "nidai tashi kikai plate dinan kitchen ki wuce kije kiyi wanka, haka akeso mace tadinga yi idan tagama aikace aikacen gida ko girki, wuce daganan sai kiyi salla" tashi tayi tadau kwanon tafito saida taje ta ijiye a kitchen sanan takoma dakin ta wanka tayi tanajin dan ciwo ciwon ciki kaman MP dinta zaizo, fitowa tayi ta tsaya gaban madubi ta kalli kanta tawani kara haske fatar jikinta na kyalli sabida man da Hajiya tasaimata mai bala'in kyau ne, tamadanyi kiba, wanan kumburin kukan da idanunta keyi a gidansu duk babu yanzu, gama shafa man tayi batabi takan kalaban kanta dake lilo ba dan batai parking nasu ba tawuce wardrobe dinta wani dogon riga tadauka na kanti mai kyau pitch color ne tasaka kawai ajiki batare datasaka bra ba sanan tasa hijabi tai salla, tana zaune kan dadduma tana biya karatun da aka mata aka kira isha'i tashi tayi tayi sanan tamike tsaye cire hijabin tayi ta ijiye kan kujera tadauki wayanta dake gaban madubi tawuce tafito, kasa ta sauka, ganin babu kowa a falo yasa tawuce dakin su Razika dake nan akasa, zaune suke su biyun suna assignment dinsu dan malamin su yabasu assignment, suna ganinta duk suna dagokai suna kallonta, murmushi tayi tace "kuma anbaku assignment" dukansu gyadamata kai sukayi, fadawa kan gadonsu tayi tace "to kugama bari nai chatting dasu Aneesa" saida suka gama sanan Razika tarufe book din ta ijiye tana kallon gashinta tace "yaushe zaki kwance kannan gashinan harya soma kwance kanshi sabida gashibki nada santsi" yatsine fuska tayi tace "ni bazan kara zuwa saloon dinan ba suncika kallon mutane wlh" dariya daga Razika har Shemau sukayi dan yanda tai maganan zaka dauka yarinyar ce harda dan turo baki She looks so cute, matsowa gaban gadon Shemau tayi tace "ai sabida kinada kyau ne saisa ake kallonki Du'a mu ana kallonmu ne Razika"? Girgizakai Razika tayi alamun a'a, yatsine fuska Du'a tayi tace "wlh ko bansan kyan nan, uhm, bari naje na kwanta" tai maganan tana tashi daga kan gadon tamike tsaye, hannunta tasa tadauki wayanta sanan ta musu murmushi ganin yanda suke kallonta tace "saida safe" "Allah tashemu lpy, Du'a gobe kezaki break" bude kofan tayi tajuyo cikeda murna tace "dagaske?" gyadamata kai Razika tayi tace " eh" fita tayi tana murna, Shemau ta kalli Razika tace "Razika daman haka takeda nono ni wlh nadauka breziya ce ke sa nononta yay girma a riga irin push up dinan sai yanzu naganta da ba breziya ajikinta" tashi Razika tayi tana gyara gadonta tace "haka takeda su harda bombom ma kaman ita tai kanta, wlh inason yarinyar sosai Shemau mugun burgeni take, dan she's so simple, batada wani ji da kanta sabida tanada kyau kaman yanda masu kyau keyi dinan kiga suna daddaukema mutane kai sabida sunga sunada kyau, Du'a ga kyau ga kamun kai ga natsuwa bakiga ko saurayi batada shi ba" Gyadamata kai Shemau tayi cikeda gamsuwa tace "hakane, Allah yabata miji kyakkyawa irinta, ni wlh daurewa kawai nake dabana tsareta da idanu dan wlh bangajiya da kallonta" murmushi Razika tayi tace "bacci nakeji". Fitowa daga dakin Du'a tayi tana murmushi tana tattaba wayanta dan Aneesa ce kebata dariya tana kawomata karan Mariya waita sace mata zobenta, typing yakuri tayi sanan ta ijiye wayan kan dinning tawuce tana tafiyan nan ahankali takarasa gaban fridge din dake dinning din tabude dan kishi takeji sosai, wani karamin bottle water mai sanyi taciro tana kallon goran, maida kofan fridge din tayi tarufe kafin ahankali tashiga bude marfin goran sanan takafa ahankali abaki tawani lumshe ido tanasha. "you know cold water is not good for the body" kaman daga sama taji murya kaman na Sharif akanta, dawani irin sauri tabude idanunta tareda juyowa, yana zaune kan dogon kujera shi kadai a falon yana sanye da 3quater na sojoji da farin t-shirt yana rike da system dake kan cinyanshi, dudda taga ba kallonta yakeba amman saida taji wani irin kunya dasauri ta ijiye ruwan sunnar da kanta kasa tayi amugun kunyace tace "Ya Sharif ina yini" batare daya kalleta ba still yana aikin dayakeyi ne yace "hope u good" gyadamai kai tayi ahankali tama rasa mezata ce tace "uhmm kaga Grandma dina? Tana sama bari nakira maka ita" tai maganan tana fitowa daga dinning tai stairs dasaurinta harda dan gudun ta, wani irin turgudewa tayi kafanta ya lankwashe dayasa tasaki wani irin wawan ihu. "wayyo Allah na kafata" tashi Sharif yayi daga kan kujera dasauri yawaigo daidai lokacin Grandma datagama wayan datakeyi tafito kenan taji ihun ta tazo stairs din dagudu tace "subhanallahi maiya faru? Muga kafan" Hajiya tafadi dasauri tana karban kafan da Du'a takasa ijiyewa kasa tsabagen azaba tana dan kuka mara sauti dan yamugun mata zafi, cikeda tausayinta Hajiya tace "sannu ijiye kafan nagani" gyadamata kai tayi tana kokarin ajiye kafan akasa wani irin ihu tayi saikuma tafashe da kuka sosai wanan karan mai kara tace "dazafi Grandma" cikin dan fushi Hajiya tace " kinsan wajen nan bene ne akan wani dalili zaki dinga gudu akai eh" cikin kuka sosai tana kokarin kama hannun Hajiya dake liliyamata kafan tace "zan kiraki ne naga Yaya Sharif yazo" cikin fada Hajiya tace "Sharif da tuntuni muke tare muna hiranmu har tuwo yaci, sama nazo nayi waya, koma bansan yazo ba gidan nan ba Bakin Sharif bane har sama zai iya zuwa wajena, Sharif zo dan Allah kadubamin kafarta kotasami targade ne, kosu Razika basu kadai ba duk wanda zaizo gidan nan hanashi gudu nake akan bene dan hatsari ne da bene yanzu jibi", karasowa wajen Sharif yayi dawani irin sauri takai hannunta ta share hawayen daya bata fuskanta, Hajiya data matsa gefe tace "au uban kukan dayagamaji kinayi dan yazo nanne zaki wani goge hawaye" turo baki tayi ta dauke kai, Hajiya tace "kaji Sharif dubamin kafan kagani" ahankali yakai yatsunshi biyu yadaura kan kafar datai ja sabida turgudewan yanabin dogayen feet dinta da kallo yace "does it hurt" yadan dagakai yana kallon fuskanta, hadiye zafin tayi tagirgiza mai kai alamun a'a hakan yasa Hajiya tace "kafan dakika gamawa kuka ne kike cewa baya zafi"? Murmushi yadanyi yace "buguwace kawai tashafa man zafi zai daina mata zafi" yay maganan yana sauka kasa abinshi, hararanta Hajiya tayi tace "wuce kije kishafa robb akai Allah kika karamin gudu agidan nan saina saba miki Du'a, kidena guje guje kinji" gyadamata kai tayi ashagwabe tace "tom" "wuce kitafi dakin ki, wani aiki Sharif ketayani yi" gyadamata kai tayi tawuce ta tafi tana tafiya ahankali Hajiya tabita da kallo saida taga tabude daki tashiga sanan tasauko tace "Allah kyauta" karasowa tayi tazauna kusada Sharif tace "wai shi gogan bazaizo yagaidani bane" dariya Sharif yayi yana abinda yakeyi yace "finally kinyi admitting kinyi kewan Asad" hannu tadaga kaman zata dakeshi ya kyalkyace da dariya yace "wlh aiki sosai ne aikin nan dayakeyi shi kanshi yagaji kinsan Asad ya tsani takura shida yasaba saidai yatakurama mutane shi baiso atakuramai Allah Allah yake gobe tayi yagama, da sassafe fa yake fita kullum" murmushi Hajiya tayi tace "Allah sarki Asad, kana ganinshi haka akwai kwazo da zuciya" murmushi Sharif yayi yace "nidai idan yazo kicemai wlh yafito da mata yay aure inba hakaba dudda ina kanninshi aure abuna ni zanyi na barshi" yay maganan yana batarai, wani irin baki Hajiya tasaki tana kallonshi tace "ohhh jama'a yauni naga takaina, kaiwai mara kunyan inane Sharif, yoo dan kaniyan kama duka duka da wata nawa ya girmeka wata uku ne fa tsakaninku haka Amminku tagayamini, Asad nada wata uku aduniya aka haifoka" dan dariya Sharif yayi yaturo baki cikeda rashin kunya yace "nidai gaskiya nafadi muku aiko Ammi nagayamata ni wlh aure nakeso kuma shi Asad banga alamun ya shirya aure ba Hajiya wlh yaron nan kaman aljani shi yama tsani mata, basa gabanshi the only matan dayakema murmushi yayi hira yay wasa dasu aduka fadin duniyan nan guda biyu ne daga ke sai Ammi, kinsan ko Anty Turai kanwar Abban mu bayama murmushi cewa ma yake he hates her, to ina zan tsaya jiran irin wanan saiyay aure zanyi ai namutu tuzuru hakanan Hajiya wlh a'a" wanan karan hannu Hajiya takai ta dakamai duka abaya dayasa yakusan sakin laptop din yace "aashhh" dauke laptop din tayi tace " naga alama kwana biyu ban jibgeka ba saisa bakada kunya, mugama aikin dakakemin Allah sa ba shirme kakeba dan naga hankalinka baikai" tai maganan tana saka glasses a idanunta tana kanne idanu danta karanta report din daya rubuta mata, karban system din yayi yace "ni dai tsaya na karanta miki natafi gida nai waya da budurwa ta kuma saina gayamata kece duk kika cinye mata time" dariya tayi tace "kagaya mata hala tamadan soka sabida yanda ba'acin kudinka at least ni Kakar ka ina moreka" dariya yayi sosai sanan ya shiga karantamata..... wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR Free Page EPISODE 2️⃣4️⃣ yauma kaman kullum suka tashi suna breakfast malamin su yazo ta tafi wajen nata su Razika ma haka, as usual by 1 yatafi, daki takoma ta kunna TV tunani kala kala aranta, wanan sanarwan nan na iya tasake saurara rasa abinda zatayi yasa tabude kofa tafice daga dakin, dakin Hajiya tabude tashiga dake meeting a zoom na retired lawyers, ita kebada report din ga glasses akan idanunta, kallon Du'a dake kallonta tayi hakan yasa Du'a tashigo wani book dake kusada ita tadauka rubutu tamata sanan tabata kallon rubutun Hajiya tayi ta gyadamata kai tareda daukan purse dinta ta zaro 10k tabata, karba tayi cikeda jin dadi tafito daga dakin sanan tasauko kasa da sauri tana murna tai wajen Razika dake dakinsu tace "Grandma tace kirakani saloon jeki shirya nima bari na shirya" gyadamai kai Razika tayi tace "kinbar wayan ki a dinning tun jiya" murmushi tayi tace "zan dauka nasan Su Aneesa ne bari naje na shirya" sama tayi, shiryawa tayi cikin wani black abaya mai kyan gaske, sanan tazauna tai rolling veils dinta dayay kyau shima ta feffesa turare tafito rikeda handbag, a falo tasami Razika tace "yauwa kin shirya muje to" gyadamata kai Razika tayi suka fice, driver Hajiya ya kwashe su zuwa wani saloon daba na ranan nan ba dantace dagaske bazata wanan ba, tsife mata kalaban akayi sanan aka wanke mata kan sai murmushi take ta kosa agama, gamawa akayi aka mata blowing hair din yabushe tass sanan matan tace "Hajiya wani style za'a miki" dasauri Razika tace "asake mata kalba amman yan kanana kanana this time" dasauri Du'a tace "a'a ayi manya manya" dasauri Razika tace "please amiki kanana Du'a ai tanada sauri" dagakai Du'a tayi takalli matan tace "idan kikai kanana zaki gama kafin 4" kasa magana da kyau matan tayi sabida idanun da Du'a ta zubamata yarinya kaman ita tai kanta. "eh bakice komiba zaki gamamin kafin 4" kasa magana matan tayi sai kawai gyadamata kai datayi murmushi sosai Razika tayi tace "kingani na gayamiki za'a gama, afara to amata mai kyau mai style" fara mata kalaban matan tayi tana mamakin yawan gashin Du'a dakeda tsayi, tsayin shikecin lokaci ma ba asalin kitson ba, wajajen 3 Du'a takalli uban tulin gashinta da ba'ayi ba tace "3 yayi sai yanzu mukai rabi" kallon fuskanta matan tayi ganin Du'a tayi kaman zatai kuka yasa dasauri tace "yakuri gashinki nada tsayi sosai ne gashi robber hair, I am going as fast as I can, zan gama dawuri" gyadamata kai kawai Du'a tayi matan tacigaba da kitson da saurinta, tanaji tana gani 4 yayi ana kan kalaban ba'a gama gamaba sosai taji hawaye yazo mata amman ta daure tahana kanta wuraren 5 matan tagama, tashi tayi tsaye da sauri tana parking kitson da ribbon dinta tadau gyalen ta ta tafa wanan karan batama tsaya rolling ba duka kudin da Hajiya tabata tabama matar sanan takalli Razika tace "muje" tashi Razika tayi suka fito tace "wai ina kike sauri zakije ba gida zamuba" girgixa mata kai tayi suka shiga mota, tace "dan Allah transcorp hotel zaka kaimu" sanan tajuya takalli Razika tace "program liyafa akeyi na matasa kan fara sana'a tun karfe hudu aka fara" gyadamata kai kawai Razika tayi dan batasan wani program bane ba akeyi ba but yanda taga Du'a tasan it must be something very important to her. Tunda suka shiga hotel din gabanta ke faduwa sosai parking yayi hakan yasa suka bude suka fito suna kallon kofan dazai sadasu to asalin cikin hotel din da wani security guard dake sanye da uniform ke tsaye yana kallonsu, kallon Du'a dataga ta tsaya sakakau Razika tayi yanda take kalle kalle tace "a ina akeyin abun" dan zaro idanu Du'a tayi irin na asalin wanda doesn't have any idea akan abu tayi tace "nima bansani ba" ganin haka yasa Razika tadan matso kusada ita murya chan ciki tace "to ki tambayi wanan security daman gashinan yanata kallonki" dan zaro idanu tayi saikuma tajuya takalli mutumin dake kallonsu har lokacin kafin Du'a tai magana yace "are you here for the program"? Gyadamai kai Du'a tayi batare datai magana ba, yace "to ku shiga hall din ma 8th floor" gyadamai kai tasakeyi sanan tawuce tafara tafiya tana kama hannun Razika suka shiga ciki tare, tunda taji 8th floor yasa tasan akwai elevator hakan yasa sukai hanyar stairs suka farabin bene, da sauri sauri gudu gudu take hawa stairs din, sosai sukai nisa dafa bango Razika tayi tana nishi sosai tace "wayyo Allah na kafana, Du'a nagaji wlh" kaman zata fashe da kuka tace "nima wlh nagaji kinga ankusan gamawa dan Allah muje" tashi Razika tayi tana nishi suka cigaba dabin stairs din ita karan kanta Du'a daurewa tayi kaman kaman kafafunta zasu tsinke, ahaka suka kai floor din tundaga tsayin corridor wajen sukaga mutane sunyi layi hadaddun yammata da maza anyi layi har zuwa hall din da cikin hall din da ake asalin abun, ganin anbisu da kallo yasa Du'a tabi Razika da kallo saikuma takoma tabayan Razika tana sussunar dakai kaman mara gaskiya dan wani iri takeji idan ana kallonta, murya chan kasa kaman mai whispering tace "Razika tambaya mana inane hall din me akeyi anan" dan Jim Razika tayi saikuma ta kalli wata mata dake tsaye alayi tana sanye da hijabi tace "dan Allah inane hall din" hall din dake gabansu matan ta nuna mata tace "ga hall dinan" ahankali Razika cikeda tausasa murya sabida karta gaji da ita tace "angama ne me kukeyi alayi dayawa haka"? File din dake hannunta matan ta nunama Razika tace "anriga angama liyafan, layin nan kuma na masu son irin su email dinshi ne sanan muna using opportunity din muna submitting CV dinmu akwai possibility na zaiyi recruitment koma baiyiba tunda gwamnati sunsan da zamanshi zaya iya sama mana aiki kingane, long layi ne about 100 people naciki duk sunata bashi kuma ya karba" gyadamata kai Razika tayi tace " nagode sosai, sanan tadan matsa baya still Du'a na labe abayanta tace "kinji ko, ina zamu iya jiran this plenty mutane dasunkai 200, Hajiya tasan kinzo nan" girgixa mata kai tayi alamun a'a, hakan yasa Razika tace "to gaskiya ki wuce mutane tunda anriga angama bazamu kafin akawo kanmu goman dare tayi" gyadamata kai Du'a tayi asanyaye Razika tace "muje" juyawa tayi ahankali suka fara tafiya saikuma ta tsaya Razika takalleta tace "menene?" ahankali tace "I want to say thank u" bata jira amsan Razika ba tawuce wajen da saurinta tai gaban hall din tana sussunnar dakai batai wata wataba kawai ta danna kanta ta kutsa tacikin mutanen dake layi tashiga hall din, tana shiga yan waje sukahau ihu chaaa barinma matan wasu suka biyota ciki ganin haka yasa tawani irin kwasa da gudu dan hall din nada makeken girma sunachan kan stage, dagudu itama Razika tashigo tana kwala mata kira. "Du'a, Du'a, Du'a ina zaki"..... Chak ya tsayar da rubutun dayake ma wata a littafin data bashi, yau yana sanye cikin wani gray suit dayafi na kullum mai kyau, yana zaune yadaura kafa daya kan daya agaban wani hadadden table, both sides dinshi bodyguards ne tsaye rike da gun, sai wasu manyan mutane dake kan stage din suma a zazzaune da suit, tsayar da rubutun chak yayi batare daya dago kanshi ba jin ana ihu da hayaniya a hall din amman suna daya kunnenshi ya iya karba Du'a! Dawani irin gudu Du'a takaraso gaban hall din daidai inda mutum zai fara hawa yan kirgaggun stairs din dazai sadaka to stage din wanda anan line din yafara duk wanda yazo kanshi xaihau stage ne yaje yasauko, wani irin tsayawa Du'a tayi tana nishi sama sama kaman kirjinta zai fashe sabida gudun datayi tana kallonshi ganin yes yes tabbas shine, daidai lokacin matan dasuka biyota suka karaso cikeda fada sukace. "ke waye dazaki baromu alayi ki gudo ki shigo ciki" juyawa tayi tasake kallonshi cikin muryanta mai shegen zagin nan da dadi dake rawa kuma sabida tsabagen tsoro dakuma gudun datayi tana kallonshi still tace "thank u" duk binta akai da kallo ganin yanda take kallonshi tacemai thank you, wani mutum dakebinta da kallo ne dakekan stage din yace "Pretty lady ki koma kibi layi idan akazo kanki then you now tell him thank u, as it is so many people sun cemai thank you yours is not first kinga he is busy" yanuna mata Asad dayama cigaba da attending to mutane kaman ma baisan something is going on ba, gyadama mutumin kaitayi hawaye na neman zubomata amman ta daure tana kallonshi ahankali tace "thank you for saving my life" daya daga cikin matayen dasuka biyota ne tawani finciketa tace "dalla malama kizo kifita" dasauri Razika takama hannun matan tace "kisaketa dalla kema ai tafiya zamuyi, muje Du'a" kasa daga kafa daga wajen Du'a tayi tana tsaye kaman an dasata tana kallonshi, muryanta wanan karan narawa sosai hawaye yacika idanunta sosai tace "thank you for saving my life" fincikanta matan tasakeyi hakan yasa Razika tace "malama dalla kisaketa, Du'a let's go" kin motsi Du'a tayi kaman ba ita akeja ba, nan hall din yadau hayaniya, ahankali ya sallami guy din dake gabanshi sanan yajuyo da kanshi ahankali yadaura fararen idanunshi akan na Du'a da akeja taki tafiya tana kallonshi, faduwa gabanta yayi yanda yanda ya kalleta, wani irin yatsine fuska yayi sanan yadauke kanshi daga kanta yajuya yakalli security dake gefen damanshi batare daya kalleta ba yana jiran next person dake kan line yanuna Du'a da yatsanshi a wulakanci yace "fitarmin da yarinyar nan daga hall dinan please and throw her outside this premises". wanna talk to me no problem just click on this link wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 Chat me up directly by clicking on this link wa.me/+2347012181461 ✍️ M SHAKUR Free page EPISODE 2️⃣5️⃣ Ko karasa maganan baiyiba katon bodyguard dinshi yataho hakan yasa Razika tawani ja hannun Du'a da duka karfinta, fashewa da kuka sosai Du'a tayi Guard din nabinsu Razika najanta da sauri tana kuka mutanen wajen namata dariya suka fita daga wajen sukai hanyar staircase suka farabi, sai alokacin bodyguard din ya tsaya ata gaban stairs din yace "idan kuka dawo cikin wajen nan saina bindigeku" dasauri Razika kejanta suna sauka sai alokacin tasan ashe kafafunta sun gaji, sosai take kuka Razika tace "waike bakida wayaune Du'a saikace wata karaman yarinya, jibi yanda kikasa akai embarrassing namu" da kyar ta iya karasa sauka daga stairs din kaman kafafunta zasu cire daga cinyanta suka fito waje, wani Alhaji ne suka gani tsaye awajen yana gyara zaman malum malum dinshi yana kallonsu, hannu Du'a tasa tai wiping hawayen dake kan fuskanta tass, wani irin murmushi mutumin yasakin mata yace "common pretty girls basa kuka, daina kuka" dasauri Razika tacigaba da janta da sauri dan magrib yayi, da dan gudinshi ko kunyan mutanen dake wuce su baiyiba yasha gabansu yakalli Razika yace "I guess ke kawarta ce ko dan Allah sakin mata hannu kibani minti daya nai magana da ita" yakalli Du'a data dauke kai yace "Pretty dance mata tasakin mata hannu" cigaba da tafita sukayi yana binsu har sukakai mota, bude motan Razika tayi Du'a tafara sawa aciki sanan tashiga itama taja kofa mutumin na bubbuga kofa takalli driver Hajiya tace "muje wanan mutumin na binmu" kunna motar yayi yaja shikuma mutumin yadaga hannunshi sama kaman mai kiran mutane saiga wata hadaddiyar jeep yazo baya yabude yashiga yace "mubi wanchan motan Auwallu amman ahankali zamubi motan sabida karsu sani suboye inaso nasan mahaifin yarinyar nan" yana biyedasu har suka shigo estate dinsu, nesa dasu yasa aka kashe motan ya gyara zama yana kallonsu, gate aka bude musu suka shiga ciki sanan aka maida gate din aka rufe, dasauri yace "tada motan kaga Auwallu" tasa motar driver shi yayi zuwa gidan da Du'a ta shiga, parking yayi akofar gidan sanan yabude bayan motan yafito yana gyara zaman malum malum yana leken gefen gate din kaman wanda yasami matsalan tabin hankali, ahankali yakai hannunshi zaiyi knocking gate din aka bude gate din aka fito, Sharif ne yafito daure da alwala dan masallaci zaije sallan isha'i, tsayawa yayi yabi mutumin da kallo, dasauri mutumin ya shiga leka gidan kaman zaiga Du'a ta gefen Sharif, ganin haka yasa Sharif yarufo gate din ahankali yace "lpy" wani irin murmushi Alhaji yayi tareda shafa kanshi saikuma yace "wai mugaisa wlh duk na rude ne naga abinda raina ke matukar so" yamikama Sharif hannu, kin bashi hannu Sharif yayi yana kallonshi still yace "lpy maikazo nema? Kokuma nace wakake nema?" sake sosa meya Alhajin yayi yace "wlh naje ba wata yarinya yar fara haka nabiyo naga tashiga gidan nan, inataso namata magana tun achan amman dayan datake tareda ita taja hannunta tahanata magana dani wlh, dan Allah ko zan iya ganinta kokuma zaka hadani da mahaifinku dan naga kaman kai yayanta ne naganka fari kaman ita dudda tafika fari da kyau" yay maganan yana lashe baki yace "Allah yayi mace awurin nan wlh" wani irin daure fuska Sharif yayi ganin tsohon banza ne, hakan yasa yace "sunana Sharif, kuma yarinyar dakake magana matata ce, ka kama girmanka ka tattara inaka inaka kabarmin kofar gida kafin nahadaka da hukuma" wani irin kwalalo idanu yayi saikuma yadaura hannu akan saman bakinshi yace "assha ai bansan matarka bace, bansan matan aure bace wlh nagayamaka bata kulani ba inda ace takulani tagayamin tanada aure daban biyota ba wlh, amin afuwa nabarka lafiya" yajuya yashiga mota dasauri sukabar wajen wani irin tsaki Sharif yaja yabi motan da kallo yace "tsohon banza kawai" saida yaga su fita daga estate din sanan yawuce yatafi masallaci. Sharif na tsakar gida yana alwala yaga shigowansu itada Razika tana goge fuskanta da gyalen abayan dake kanta idanunta sunyi ja sosai, bama su luradashi ba suka wuce ciki, falo suka shiga kallo daya Hajiya dake zaune akan kujera tana magana awaya tamata tagano wani abu dasauri tacire wayan daga kunnenta tace "zan kiraki Hajara" katse wayan tayi takalli Du'a da Razikan da duk suke atsaye sun kasa karasowa gani suke kaman tana ganinsu zata gane abinda yafaru, yunkurowa tayi tana kallonta still tace "why did you cry Du'a? Maiya sameki?" Dan zaro ido tayi this is the first time datasan tama Grandma dinta laifi sosai, Grandma data taimaketa tabata freedom shine daga fara fita ta hartaje hotel ita maiyama kaita taje, duk ta tsaya tana tunanin nan zuciyanta fall da tsoro batare databama Grandma dinta amsaba, juyakai Grandma tayi takalli Razika tace "maiya sameta take kuka"? Baki Razika tabude zatai maganan da sauri ta tattaro duka karfinta ta tari numfashin Razika ahankali tace "Grandma hannun matan zafi sosai kuma gashi tadade kaina ke ciwo" sosai Grandma ke kallonta, ga idanun nan nata sundan kumbura alamun tasha kukan tace "to dan kanki na ciwon kitso sai kiyita kuka banace kidena all this abubuwan ba keba yarinya bace"? Gyadama Grandma kai tayi hawaye nasake taruwa a idanunta tace "sorry" ganin tana neman sake kuka yasa taidan murmushi dan she looks damn cute tace "zonaga kitson" tahowa tayi ahankali gabanta nafaduwa sosai ko kadan bataso tama Grandma dinta karya ba, zama tayi gefenta, Grandma tabude kan tana kallon kalaban dayay bala'in kyau tace "wow daman abu mai kyau yafi bada wahala, kinga yanda yay kyau kuwa, wow oya jekiyi salla kiyi wanka kizo nabaki abinci da paracetamol kisha" gyadamata kai tayi ta tashi ahankali sama, Grandma takalli Razika dake tsaye itama tace "sannu kinji Razika, Du'a dukta wahalar dake, jeki daki kiyi salla kihuta" ahankali tace "to" tawuce, tashi tayi itama dayake hijabinta nakusada ita dan tariga tai salla yasa ta tashi ta shimfida dadduma danyin salla. Takwas daidai yabaro uban mutanen dake kan layi yafito dan yagaji iya gajiya, juyawa yayi yakalli security dake biyedashi abaya yamika musu hannu yace "car keys, u can go" daya daga cikinsu ne yadauko key daga aljihunshi yamikamai yace "Sir daka bari mun maidaka gida is not safe for you to be driving alone" dan yatsine fuska yayi yace "it's okay" juyawa yayi yakunna mad ride dinshi yabude kofa yashiga sanan yatada motar, tafiya mai tsawo yayi sanan yakai gaban wani eatry, shiga ciki yayi sanan yay parking inda ake parking ya kashe motar, wayanshi yadauka ya daddanna sanan ya ijiye wayan kan cinyanshi ya jinginar da fuskanshi jikin kujera tareda lumshe ido yana fuzarda iska, Asad wani irin mutumne da idan zaka kwana kana kallonshi bazaka taba tantance wani yanayi yake ciki ba sai idan kai mai lurane. Knocking motarshi da akayi yasa yabude idanunshi ahankali yadago kanshi, wata doguwan fara mace ce tsaye gaban kofan tana sanye dawani arnen half gown daya tsaya daidai gwuiwanta sanan an tsaga tagaban da kadan yarage ba'a ganin pant dinta, kanta sanyeda attachment daya zubo har waist dinta taci uban makeup a fuska dayamata kyau ba laifi ga hill akafanta mai tsinin gaske, yarinyan dan kyau Allah yayi kyau ga hips ga boobs duka, danna lock din motar yayi kofan yabude hakan yasa tabude kofan ta shigo ta zauna tareda maida kofan tarufe sanan tajuyo takalli Asad din dake kallonta bayabo ba fallasa murmushi tamai tadan juya idanu tana chewing gum dinta tace "why call me wajen gari haka, wajen garin ma this local place, you are so lucky ma danazo" shiru yayi yana kallonta ta duhun harta gama tana wani yatsine yatsine, jin shiru yasa takunna flash din iPhone 11 pro max dinta tadaga ta haska fuskanshi tana kallonshi kaman yanda ko gezau baiyiba kallonta yake tace "woooww, bansan cewa mahaifinka nada kyakkyawan thick sexy boy hakaba, so you are the famous Asad da mahaifinka always talks about, only son, his father's pride, wowwww" cikin thick voice dinshi yace "would you mind turning that off" wani irin lumshe ido tayi kafin ahankali tasauke wayan ta kashe flash din tasan Alhaji yana yawan bata labarin Asad dinshi but bata taba sanin babban Matashi saurayi haka bane mai jini ajika ba gashi kyakkyawa yafi baban shi kyau sosai, ahankali tace "why did u call me here" shiru yamata yakai kusan 3min sanan yace "inaso kirabu da mahaifina ne!" dawani irin sauri takalleshi saikuma tanuna kanta tace "ni Zinariya kake cema narabu da mahaifinka? Sugar Dady nawa? Anya kasan girman abinda kake fadi kuwa, dakakirani cemin kayi we will talk business zakamin proposing offer da I can't resist saisa nazo, is this the offer"? Dauke kai yayi daga kallonta yajuya yana kallon waje yace "sunanki Zainab Garba Habu from kano, anguwan uku layin Murtala hamisu house number 3, mahaifinki yarasu, mahaifiyarki nada rai ita ke kulamiki da yaronki mara uba kekuma kina nan Abuja kina karuwanci dan kisami kudi kidinga turamusu....." yanda yake maganan komai waye sai wani kalan natsuwa yashigeka, batare daya kalleta ba yace "kaman yanda nagayamiki awaya I have an offer for you bana karya is true I have that offer, inaso kirabu da mahaifina is exchange ma 10million naira, gida akowani kasa kikeso acikin kasashen waje da visa da passport miki da mahaifiyarki da kannenki dakuma danki inkin yarda" tunda yake maganan jikinta ke tsuma amman tadaure tahana kanta tanuna tadai daure takalleshi tace "sabida 10million ne zan rabuda Alhaji shikemin komi, yabani kudi naturama yan uwana akan me zan rabudashi sabida yan chicken change dinan naka da balallai ne kabani ba" hannunshi yamika yadauko wani envelope daga kujeran baya yadawo dashi gabanta yabude yazaro takardan ciki yamika mata karba tayi ahankali tana kunna hasken wayanta tana dubawa maida kanshi yayi kan hanya yace "I am sure u can read, wanan agreement ne da lawyer na yarubuta nariga nayi signing inhar kin yarda zaki rabu da mahaifina kibarshi har abada without having any form of contact dashi aboye to komi dana fadamiki nakine sanan inda daga baya kikazo kika saba alkawari to inada right na na kulle ki agidan yari but all this saikin yarda ne zaki iya signing" duka abinda yafadi haka yake arubuce awajen, Alhaji nabata kudi but baitaba bata kudin dayafi 500k ba, yana bata kudi 50k 60k tasaima gidansu abinci, yasata awani gidanshi kullum ya ijiyeta cinta kawai yake amman yaki aurenta kotamai maganan aure saiya cemata shi bayida ra'ayin kara aure amman komi yamata, ga motanshi daya daya ijiye mata dudda bai bataba amman tana hawa, yanzu ga kudi malala har 10mil da rayuwa kasan waje manta manta, ubanme Alhajin ke tsinana mata banda uban jaraba yacita kusan sai shidda arana duka baya wuce 1min, sai bakin jaraba bakarfi kaman ammai baki anya bazata karbi wanan offer ba. Anjiyan zuciya tasauke dashi kanshi saida yaji, sanan takalleshi dudda aduhune bai hanata kallonshi ba tundaga kai har zuwa kan cinya, yanda gaban wandonshi yadan tattaro yataru waje daya yay tsaho kaman wandon ya kwanta kan wani luteten maciji ne yasa tawani hadiye muyau, ko Alhaji nada zankaleliyan azzakari balle danshi kawai tashi ta kwan biyu ne, Allah yamata girma gatada shegen jin sha'awa amman yana shiga yakawo abin tadaina functioning sabida tsufa amma yanzu tasamu tadan dandana yaron nan nashi ai sharrr daga ganin wanan Allah zaiyi karfi da kuzari ajikinshi, gyaran murya tayi tace "kanada pen tareda kaine" hannunshi yamika yadauki pen batare daya kalletaba dan she disgust him yatuna ita ubanshi keci saiyaji kaman ya shaketa anan tamutu, mikamata pen din tayi ahankali takarba takai bakinta tadan gatsi duwawun byron tana kallonshi yanda ko kallo bata isheshi ba, zaro byron tayi daga bakinta tace "inada sharadi daya nima, gabaki dayan abubuwan daka rubuta anan nayarda nima kuma inada sharadi guda daya tall kana yardan mini zanyi singing" batare daya kalletaba kai tsaye yace "say it" dan gyara zama tayi tanawani irin kallonshi kafin tadan ciji lips dinta tace "inaso kacini muyi one night stand I promise no emotions attach kasan aiki nane karuwanci danka kwanta dani bazaisa narikeka ba konace dole saika soni, kawai kamin ne u are so classy, young, educated, rich and above all u are damn handsome gashi Allah yamaka jiki, zaka cini din? Ina bukatan kasa na manta da mahaifinka ta hanyar zuxxubamin ruwanka adurina yakora na Abban ciki sabida na manta dashi". 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 2️⃣6️⃣ daurewa yayi iya daurewa danko kadan baiso tagane yanayin dayake ciki but maganan datayi kiris yarage bai koro amai acikin motan ba, hakan yasa yakasa magana dawuri kafin ahankali yace "it seems u are not interested in my offer, keep the paper and get out of my car" ganin yanda babu wasa tattare dashi yasa tadanyi murmushi tace "wow yanda Abban ka keda raha bansan cewa zai iya haifan murdadden mutum haka ba, anyway naji tunda u don't wanna fuck me u have to add 2min akan kudin idan kayarda then we have a deal idan baka yarda ba we don't have" yana kallon waje har lokacin yace "deal zan baki 12M" signing paper tayi sanan ta mikamai hannu yasa yakarba yace "zan aiko miki da kudinki and everything dana fadi gobe with a copy of this document dakikai signing excuse me" wani irin murmushi tayi tacigaba da taunan cingam dinta tace "I am curious so I have to ask this question kana tunanin ayanda Babanka yake sabida nabace na barshi bazai nemi wataba ne?" batare daya kalletaba yace "at least idan baki zai dawo gidanshi to his family" wani kalan dariya tasaki tana tafa hannu saikuma tanuna shi da yatsanta dayasha uban nails tace "I am sorry Asad but bari nagayamaka this kaga mahaifinka neman mata nacikin jinin shi ne, kaga dudda yana taredani nasan cewa nice best dinshi da nikadai wacce ya ijiye akarkashin shi but still bai hanashi cheating on me ba yanabin wasu up and down, agabana baya kunyan kallon mace kaman zai cinye ranan nan harwata yar kyakkyawan yarinya yadinga kallo a saloon daya kaini, kawai zama nakeda shi sabida banda wanda yake kashemin kudi irinshi but baban ka is a certified cheat" batare daya kalletaba yace "can you get out of this car please" dan dariya tayi tana kokarin bude kofa tace "sure mana ganinan ma fita nake, but know this, bin matan Baban ka kana basu kudi dan surabu dashi is not a problem dan karuwai irinmu are just after money zamu karba muwuce, the problem is kudinka gabaki daya saiya kare akan babanka ne, that Man bayason mahaifiyarka yace batada komi kaman bamace ba haka take gar........" wani irin ihu daya dakamata yasa batasan lokacin datai wani irin tsalle tafadi waje akasa daga motan ba bura'uban wlh ta bala'in firgicewa, kunna motar yayi baima tsaye rufe kofan side dinta yake abudeba yawani irin yi reverse da mugun gudu tai flat akasan wajen danda sai marfin motan side dinta ya kwaye mata fuska yawani wanke ta da kura yabar wajen. Yadade yana tuki sanan ya tsaya awani masallaci akan hanya yay salla sanan yafito yashiga mota yana tuki yana lumshe ido yana budewa, he just needs some time alone, he needs fresh air, kaman yatafi airport yashiga jirgi yabar garin yakeji amman bazai iyaba, he just wants to get away daga gidansu this night baimasan kowa ya ganshi na gidansu, yana tunane tunanen yakai anguwan su kasa karasawa yayi gidansu kawai saiya sami kanshi da tsayawa gaban gidan Hajiya horn ya danna hakan yasa Maigadi yafito ganinshi yasa yakoma yabude gate jan motan yayi ciki, yadade zaune a motan sanan yabude yafito yay ciki, ahankali kaman mara gaskiya yay sallama chan kasa yabude kofan falon yashiga, Grandma na zaune kan kujera ita kadai a falo tana kallon gidan Badamasi a Arewa24 ga bowl dake cike da sliced fruits ajikinta tajuyo da kanta, kallo daya tall tamai takarance shi tsaf, maida kofan yayi yarufe ahankali yakaraso cikin falon har zuwa gabanta ya tsaya, cikin wani kalan yanayi na bala'in sanyin jiki yace "har yanzu dakina na nan Grandma"? Duk gidansu Ammi shi kadai kecema Hajiya Grandma dan sauran gabaki dayansu Hajiya suke cemata, tunda yaga yanda Ammin shi tamaida Hajiya Mahaifiyar da Batada shi dan Ammi batada Mama, Maman Dadsuka raineta, tunda yaga yanda Ammin shi kesonta itama takeson Ammi yamaida Hajiya kakanshi saisa yake cemata Grandma, yawanci idan yana cikin kunci ko wani abu na damunshi wajen ta yake zuwa yakwana dan musamman tamai dakinshi agidan, saisa dazaran yazo wajen ta Ammi bamata nemanshi sai hankalin ta ya kwanta. Ahankali tace "Asad are you okay"? Gyadamata kai yayi batare dayay magana ba, dan Jim tayi tana kallonshi sanan tace "jeka kwanta dakinka na nan, nakawo maka wani abu ne"? Girgixamata kai yayi yace "a'a I will eat in the morning" yay maganan yana hawa stairs, falon saman yawuce da dakunan dake wajen yay wani dan corridor da aka jera flowers awajen wanda bazaka taba sani da flower awajen bama, ahankali yabude kofan dake wajen yashiga dakin dakenan fess fess gahotonshi da aka makala a bango lokacin yay graduating a school a UK dashi da Grandma ne ajikin hoton suna murmushi duka. wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR Free page chat me up by clicking on this link wa.me/+2347012181461 EPISODE 2️⃣7️⃣ Fadawa kan gadon yayi batare dayacire daidai da takalmin kafanshi ba balle kuma ayi maganan kaya, sosai kanshi kewani irin sarawa, he's so tired and everything and anything, he's working damn hard to keep his whole family happy, shi baida matsala idan da Dad zai natsu yace aure zai kara yasan Ammin shi she won't object to that dan tasan yafi mata alkhairi, but wanan wulakanta Ammi dayake yi yafi komai bakantamai rai, shi bawai yasaketa ba kotamai wani laifi ba amman saiya kauracemata dasu yaranshi for months kuma bawai yaje anywhere bane yana nan Abuja tareda matan banzan shi, yasan once Zinariya takarbi komi dazai bata gobe ta tafi zai dawo gida he hopes from there shi And Ammi can work something together, wani zubin he understands his Dad in the sense that auren hadi aka mai da Ammi but that doesn't zama excuse nashi dazaije yana Zina up and down, Ammi is very very sick low BP takeda shi ita ba high BP ba, and low BP yafi dangerous da high BP mutum can yanke jiki yafadi at any time yamutu, akanme Dad zai dinga wulakanta Ammi eh yamaida ita kaman trash his mother is very sick dudda bata nunawa, but yaga tanashan drugs aboye, gashi sai ramewa takeyi, she's depress dan yasan Ammin shi nason Dad sosai kodaga yanda take luradashi ma zakasan hakan he just wish yanada power to change things arayuwanshi, he wish ana iya chanza mahaifi, hannunshi yakai ahankali ya share wani dan gajeren hawayen daya zubomai ta gefen ido sanan ahankali ya fuzar da iska waje mai zafi, ko minti biyu baikaraba bacci yay awon gaba dashi mai nauyi gaske yana sauke ijiyan zuciya daman ance behind every thought face akwai thousands of weakness aciki. Wuraren 5:30 nasafe Grandma tabude kofan dakinta tafito, hanyar dakin da Asad keciki tayi, ahankali tasa hannu tabude kofar tashiga yana bacci har lokacin baitashi ba ga takalmi nan baicireba kayama haka, maida kofan tayi tarufe sanan takaraso tazauna abakin gadon, ahankali takai hannunta taciremai takalman ta ijiye sanan tajuyo da kanta takalli fuskanshi tana kallonshi, harga Allah tana bala'in son Asad samada kowani d'a agidan nan, why because Asad might look harsh kana ganinshi zakaga bakin halinshi but he's weaker than any other person agidan nan dan abu yafi damunshi kan kowa, gashi da zuciyan nema dudda Asad baitaba nunawa ba ita tariga tasan yasan komi gameda halin Baban shi saisa yana gama school yanemi jari daga CBN batare daya karbi kudin Babanshi ba yabude kampanin kanshi cikin ikon Allah kuma kampanin sai albarka yake, yay wayon nanne sabida duk ranan da mahaifinsu zai juyamusu baya he will be able to take care of his family, bambamcin shi da Sharif kenan, Sharif is very nice but Asad yafishi hankali da hangen nesa dudda idan angansu kowa will go for Sharif dan physically yafi kirki and more welcoming, Asad is just a small boy daya Goya responsibility alot abayanshi saisa yake bata tausayi, she just wish zai natsu ya nemi mata ya aura koyasami natsuwa amman tsoron yanemi mace ma yake sabida baiso yagaji irin halin mahaifinshi beside ance blood is thinker than water, saisa gashinan ne kawai bakowa ke ganeshi ba. Hannunta takai ahankali tashafa tattausan sajenshi tace "kai tashi kayi salla" da kyar yabude ido, ahankali yace "okay Grandma " tashi tayi tawuce tafita daga dakin, dakin Du'a ta shiga tabitada kallo yanda take baccin ta hankali kwance, karasawa tayi gaban gadon zama tayi tashafa fuskanta ahankali tace "yammatana atashi daga bacci, Du'a Du'a" da kyar Du'a tabude idanunta takalli Grandma cikeda bacci a ido batare datai magana ba, kumatunta Grandma taja tace "da ace yanda kikeson bacci haka kikeson cin abinci danaji dadi saisa kullum cikinki kaman ana diba ayi biyan bashi dashi tsabagen yanda yake ashafe kaman cikin jinjiri" dan murmushi tayi saikuma ta jinkirto tadaura kanta akan cinyan ta takama hannun Grandma dake kan fuskanta ta rungume ajikinta sosai ahankali tace "Grandma agidan ki kadai nasami farin ciki haka tunda aka haifeni, Grandma please karki bari Abba yakomar dani gidanshi I am so happy anan da I don't wanna leave, da kullum sainai kuka Ya Hamad kadai ke lallaahina da Aneela" fadada murmushin dake kan fuskanta Grandma tayi tana kallonta tace "bazaki komaba ai nagayamiki sai inda karfina yakare babu wanda zai kara wahalar min dake, yanzu addu'a na shine Allah yakawo miki miji nagari" murmushi tayi sosai saikuma ta tashi tazauna takalli Grandma tace "Grandma nina isa aure ne? Ya Nana da Ya Hawwa fa duk basuyi aure ba, kumama ai sai mutum ya iya girki akemai aure ko nikuma ban gama iyawaba tayaya zanyi aure to"? sosai Grandma ke kallonta yanda take maganan saida tagama maganan sanan taja hancinta tace "har wayauma baki gamayiba dan Aneela zata iya sayarda ke agaban idanunki baki saniba, tashi kiyi salla ki shirya yau akwai office" gyadama Grandma kai tayi tana tashi ta sauka daga kan gadontai hanyar bayi kananun kalaban da aka mata sun zubo har waist dinta suna lilo kaman wata balarabiya tabude kofa tashiga bayi, ajiyan zuciya Grandma databita da kallo ta sauke sanan ta tashi ahankali tafice daga dakin. Saida tashiga bayinma taga batada salla daman tun jiya takejin ciwo ciwon ciki, brush kawai tayi tai wanka da ruwan zafi sosai tafito daure da towel tanada feeling ciwon ciki kadan kadan dayake ita batada wanan serious ciwon aran nan saidan dan ciwon ciki kadan hakanan, wani black mickey riga tasaka, t-shirt ne amman irin na baccin nan babban gaske daya saukan mata har guiwa, batabi takan kama gashinta ba tasake shi ahaka yana lilo abinshi, komai ma bata shafa fa tasaka slippers dinta tabude kofan dakinta tafito ahankali, dakin Grandma tayi ganin bata ciki yasa tamaida kofan tarufe tai hanyar stairs tana sauka kasa, ganin Grandma zaune kan kujeran dakin rikeda Al Qur'ani tasaka glass a idanunta tana karantawa yasa takarasa wajenta zama kusada ita tayi ahankali batare datai magana ba tana sauraron yanda Grandma ke karatun anatse Akuma hankali Aya ta dire sanan takalli Du'a din alamun ya akayi, ashagwabe tana wani turo baki kaman yar baby tace "Grandma good morning cikina naciwo kadan kadan, MP ne, kinada magani"? girgiza mata kai Grandma tayi tace "bari zansa akawo miki, yanzu tashi kidebo ruwan lipton a flask kije daki kisha saikidan kwanta kafin lokacin zuwa office yayi" gyadamata kai tayi ta tashi dinning tayi cup tadauka tadauki flask ta tsiyaya ruwan shayi dayasha kayan kamshi sanan tadauki spoon tasa a cup din tawuce tai stairs tana tafiyan nan nata ahankali tana kallon shayin da kamshin shi sai ratsa mata hanci yakeyi, tsayawa tayi chak jin wani irin sanyi ya ratsa kafafunta dakenan abude zuwa jikinta gabaki daya, wani dan kara tafitar daga bakinta ashhhh sanan taduka kaman wacce zatai ruku'u tana duba kafafunta tana daga kafanta sama tana duba tafin kafan kota taka kankara ne ganin babu abinda ta taka yasa ta dago tacigaba da tafiya ahankali tana hawa stairs din zuwa karshe tashiga falon sama daidai Asad shima yafito daga corridor hanyar dakinshi yashigo cikin karamin falon yana lazy tafiyan nan irin na wayanda suka sha bacci, wani irin hada idanu sukayi dagashi har ita, chak ta tsaya tana kallonshi da duka idanunta awaje kaman zata hadiyeshi da ido, yana sanye da kayan jiya dataganshi dasu a hotel dinnan bambamcin kawai shine babu jacket din suit din da neck tie da alamu yaciresu ne, farin long sleeve t-shirt din ciki ne kawai ajikinshi daya bubbude boturan gaban rigan har zuwa kasan kirjinshi kana iya gashin kirjinshi dasuka kwanta lubbb idanunshi sundan tashi da fuskanshi lips dinshi sunyi pink yirrrr alamun yasha bacci sosai looking a bit scattered kaman ba shiba, yanda take kallonshi haka shima yake kallonta da wanan expression nashi dinan dabaka taba gane takamaimen wani yanayi yake ciki. Wani irin rawa hannun data rike mug din shayin ta dashi ne yashiga wani irin rawa tana kallonshi jikinta na bar bar da batasan mesaba takasa koda motsi, tundaga kafa yakalleta zuwa kai saikuma ya basar kaman bai ganta ba yacigaba da tafiyanshi normal normal yazo tagefenta zai wuce kamshin da jikinshi keyi yawani yi splashing akan fuskanta wani irin salubewa mug din hannunta yayi ruwan shayin ya bare some of it yazuba akan kafanta kofin yay wani kara yahau tsalle yana tsaltsalleke stairs kafin daga bisani ya tarwatse, wani irin runtse idanunta tayi gam jin yanda kirjinta ke bugawa dum dum kaman zai fita jinta kusada shi kaman jikinshi zai gogi nata yattsun kafanta namata radadin zafi amman takasa ihu sabida yanda tashiga wani yanayi, wani irin beating kirjinta yakeyi tanajin sahun tafiyanshi yanabi ta gefenta yawuce yay stairs abinshi mayen kamshin turarenshi yagama wanke mata numfashi yasauka daga stairs din yay falo abinshi. Sai alokacin tabude idanunta wani irin zama tayi a kasan wajen dagudu takama kafarta tadaura akan cinyanta tana hura yatsunta dake mata radaddin azaban zafi sosai tana kuka sosai amman mara sauti tana hura kafan....... Zama yayi kusada Grandma dake karatu abinta har lokacin, murya chan kasa irin nawanda yasha bacci sosai yakoshi dinan yace "good morning Grandma" saida takai Aya sanan tai addu'a tarufe Al Qur'ani takalleshi tace "wanan bacci dakasha haka kaga yanda kai subu subu kuwa kaman wanda yay kwana uku yana bacci" dan murmushi yamata tareda lumshe ido yabude baice komiba, tashi tayi tace "bari kaga nakawo maka shayi mai zafi kasha zaisa kadan saki ko" gyadamata kai yayi yana kwanciya kan kujeran data tashi kaman wani dan yaro, itakuma tai hanyar dinning harzata wuce saikuma idanunta suna sauka kan mug daya gangaro zuwa nan stairs na kusa to the last dasauri takalli sama ganin Du'a zaune tana hura kafa tana share hawaye yasa tace "subhanallahi Du'a meya sameki kike kuka haka? Ince badai kin koma kafarki ba shine baki kirani ba" tai maganan tana hawa sama, tana kaiwa wajen takarbi kafan tana kallo aiko gashi nan yatsun sunyi jajir alamun sunsha ruwan zafi, hannunta takai takama kafadar Grandma tana kuka sosai mara sauti tace "Grandma zafi wlh" dasauri Hajiya tashiga kwalama Razika kira. "Razika Razika" Razika dake daki fitowa dagudu tari jin Hajiya na kwalamata kira, turus ta tsaya afalon tana kallon Asad dake kwance abinshi idanunshi bude kaman yasan ta inda zata fito kenan kallonta yayi shima, fitowa Shemau tayi ganin Asad yasa dasauri tadan rusunna tace "ina kwana" gyadamata kai kawai yayi batare data amsaba hakan yasa Razika itama tace "ina kwana" ko kallonta baiyiba yadaura idanunshi kan TV dasauri duk sukai stairs, Grandma tace "kawomin zuma Razika Du'a tazuba shayi akafa" dawani irin sauri tajuya tace " to" zuman dake dinning tadauko tadawo sama, karba Grandma tayi tashafamata sanan takalleta idanunta sunyi jajir tace "sannu dena kukan to" gyadama Grandma kai tayi tana share fuskanta takalli Razika tace "kaita dakinta ke Shemau biyoni ki debi wani shayin ki kaimata saiki gyara wajen nan" duk amsawa sukayi da to sanan tawuce kasa, Ganin Asad na nan inda tabarshi yasa tace "wai jikata ce shayi ya bare ayatsun kafarta take kuka shegen raki irin na Du'a bawani konewan kirki bane bafa, itace jikata datazo daga kano yar wajen Zainab, bari kaga nabaka shayin ka". 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR This book is 500 nakusan gama free pages, you can join the group by paying 500 into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turo evidence of payment ta watsapp number na wa.me/+2347012181461 sainai adding naki to the group. free page EPISODE 2️⃣8️⃣ Zubomai shayin tayi a mug dakanta sanan tadawo kusada shi kafanshi tadauka tace "sit up my friend" dan murmushi yamata yatashi yazauna tareda mika hannu yakarbi shayin yace "thanks Grandma, you are the best you know that right" murmushi tamai tace "nasanar da Ammin ka kana nan, ya TV show dakayi angama lpy"? yatsine fuska yayi yakurbi shayin kadan yacire daga baki yace "it was stressful but Alhamdulillah nagama" dan dariya tayi tace "kai Asad, yanzu dai mezan dafamaka yau kaci ka koshi" ahankali yace "rice and beans nakeso Grandma" "kaida shinkafa da wake Asad shikenan zan dafamaka" murmushi yamata yace "Grandma bakiyi fushi dani ba tunda nadawo banzo ba" hararanshi tayi tace "ja'iri ashe kasan kayi laifi" dariya kadan yayi yana kurban tea, tace "ai nayi fushi dakai but Sharif nata gayamin how busy u were saisa andena fushin, yanzu daka gama bagaka kazo ba, ai ba'a raba jika da kakanshi" hira suka cigaba day haryana bata labarin aikinshi sosai taji dadi yanda yasake dudda batamai maganan abinda yasameshi jiya ba, saida yagama tass sanan ya ijiye cup din yace "Grandma bari naje na shirya natafi office, I have huge work awajen ma" tashi tayi tace "tafi Asad, Allah yataimaka kaji, nidai kadingayi kana neman mata inaso naga jikana kafin namutu" yatsine fuska yayi irin ewww dinan bayamason maganan sanan yawuce yafita daga falon yatafi itakuma Grandma takoma tai zamanta dan akwai shirin dazata kalla. ** Zaunar daita Razika tayi akan gado sanan takoma tarufo kofa dagudu tanadan zaro idanu tace "naga mutumin jiya a falo Du'a biyomu yayi ne" cikin tsoro muryanta dabai gama washewaba sabida yanda tai kuka tace "nima shina gani bansan lokacin da kofi yafadi daga hannuna ba yanzu idan yafadi ma Grandma Yaya zanyi? Wai waye shi? Ya akayi yasan Grandma sosai har yafito daga lungun flawas din falon saman nan eh" hannu Razika tabude itama alamun oho cikeda damuwa tace "oho amman kaman Shemau tasanshi naga ta gaidashi da sauri tana ganinshi kinsan ita tadade tana aiki agidan nan ni ba'a dade da kawoni ba" shiru Du'a tayi har lokacin gabanta faduwa yake, zama kusada ita Razika tayi murmushi tayi takalli Du'a tace "sonshi kike ko Du'a"? wani irin kwalalo idanu waje tayi tace "so kuma" gyadamata kai Razika tayi tace "eh naga yanda kike ta kallonshi jiya ana koranki kinki tafiya kinata cemai thank you for saving my life keda bakima sanshi ba, sonshi kike ko? Yanada kyau sosai wlh gashi dan gayu gashi mai kudi har ana nunashi a TV, sonshi kike"? Girgixamata kai Du'a tayi tace "a'a kawai nasanshi ne tun a kano, shine yataba cironi daga rijiya saisa dana ganshi nace sainaje namai godiya" gyadakai Razika tayi da gamsuwa tace "to Allah sa shiyace yana sonki wlh danaji dadi" dan daure fuska tayi tace "ni banson maganan nan" yatsun kafarta dahar jan dasukayi yasoma washewa takalla tace "bazakije office ba? naga yatsun harsun washe kinga yau Monday fashi ranan Monday is a serious offense" Yatsun itama takalla tace "yadena zafi, tayani zabomin kaya kinga banda lafiya saina shirya natafi" hannu Razika tasa ta dungure mata goshi tace "kewai mai wayau ko" tai maganan tana zuwa gaban wardrobe dinta wani ja da bakin abaya taciro mata sabo fill tana kallonshi tace "wowwww abayan nan yay bala'in kyau, Hajiya tasai miki"? murmushi tayi tana girgixa kai tace "Aneesa tazaban min ranan damukaje shopping yay kyau" warware rigan Razika tayi tace "wlh kam yayi kyau kai yayi bala'in kyau ma, oya tashi kizo ki shirya" tashi tayi tana kallon yatsun nata jin sundena mata zafi, wucewa Razika tayi tafice daga dakin tace "saikin fito" tom Du'a ta amsata tana kokarin cire rigan dake jikinta sanan ta ijiye ta shirya cikin rigan kafin tazo gaban madubi tatsaya tana kallon kanta for the first time yau taga kyanta da ake fadi ja da bakin color ya bala'in mata kyau, zama tayi tana daukan ribbon parking kitsonta tayi a tsakiyan kan yay kaman acucu gashin goshinta sun wani irin bala'in kwanta, sanan tai rolling gyalen abayan, man baki talakata ta shafa a lips dinta dayay wani pink sanan ta tashi tana hada jakanta tadau pad tasaka dakomi da Grandma takoyamata sanan tazura wani flat takalmi mai budadden sama daya bayyana fararen cute kumbunan kafanta, ahankali tasa hannu tabude kofarta tana lekawa gabanta nafaduwa ganin babu kowa yasa takarasa karasawa wajen bene tashiga tafiya ahankali, Grandma kadai tagani zaune tana fere apple dawani karamin wuka, dago kanta tayi jin sahun tafiyanta, kasa daurewa tayi sabida yanda tai kyau tace "Masha Allah tubarkalla Du'a kinyi kyau sosai har kafan ya warke ne"? murmushi tayi tana zama kusada ita tana gyadamata kai, Hajiya tace "to dama banda shegen shagwaba naki ruwan lipton wani konewan kirki ne, kedai kawai rakin ki yay yawa, tashi ki tafi aiki yau Monday aka ciki taran latti baruwana wanan da Ogan ku yadawo ai kunbani" dan zaro idanunta tayi sai yanzu ma ta tuna Sharif yacemata this Monday Ogan su zaiyi resuming office, zumbur tamike tace "bye Grandma" murmushi Grandma tayi tabita da kallo sabida yanda yarinyar tai kyau tace "ayi addu'an fita daga gida Allah tsare" tsalle tayi kaman yar yarinya tace "tom" "kidena tsalle" Grandma tafadi tana murmushi ganin yarintarta. Motan Grandma tashiga zama tayi driver yajata sai alokacin ma ta tuna batai breakfast ba, har campanin yakaita, yau kawai taji tana having wani irin wired feeling kaman tace sujuya su koma gida kartazo aikin. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR free page EPISODE 2️⃣ 9️⃣ Parking driver yayi awajen parking motoci yana kallonta ta glass haryau yakasa daina mamakin inda Hajiya tasamo kyakkyawan yarinya haka a jika, yasan Zainab(Mami) baka ce to kodai mijinta irin fararen yan shuwa arab dinnan ne, bude kofa tayi ahankali tafito sanan tajuya tadauki wayanta da jakanta screen din wayan dayay haske ta kalla ganin 15mins after 9 nasafe yasa taji jikinta nadan rawa dan bata taba latti ba kuma batasan ko boss din nada kirki ba karya mata fada, maida kofan tayi ahankali tarufe tace "thank you Uncle" dan haka take kiranshi sanan tajuya tafara tafiya zuwa entrance sanan tashiga ciki, Sharif tagani tsaye gaban kantan reception yana sanye cikin cooperate kaya ba suit ba amman wando da riga yay tucking ga belt dayasa mai kyau yana duba Rolex din dake daure a wrist dinshi kaman akwai abinda yake jira, kaman yaji ajikinshi kallonshi ake yasa yadago kanshi yakalli entrance hada idanu sukayi ajiyan zuciya yasauki sanan yasakin mata wani irin cute smile yana dumfaro ta, saida yakai gabanta ya tsaya ahankali yace "you look ahhhhh mema zance"? Yay dan shiru yana kallon sama yadaura yatsanshi daya kan kumatunshi kaman mai tunani saikuma yakalleta ganin yanda take kallonshi irin ta kosa taji mezaice dinan yasa cikeda tsokana da wasa yace "you look like indon kauye" gabaki dayan murmushin datakeyi bacewa yayi tai raurau da idanu kaman zata fashemai da kuka hakan yasa yay dan dariya yace "just teasing you" saikuma ya tsareta da idanunshi da for the first time tunda tasanshi suke shiri sosai tana kallonshi kaman yayanta taji wani iri hakan yasa tadauke kanta, murya chan kasa yace "you look damn cute Du'a kaman in saceki in gudu" murmushi tadanyi kanta akasa dan tasanshi da wasa still tana wasada yatsunta, for a moment yamanta inda suke tsaye all yake gani wasa her tsaye agabanshi, ahankali yadan waiga yabi wajen da kallo sanan yajuyo yakalleta yace "I've been calling you baki dauka maisa" dago kanta tayi takalleshi ita bamatasan tayaya yasami number taba, saikuma tanunamai wayannata dake hannunta tace "anan ka kirani"? Wayan ya kalla yace "yes, I gave u about 3 to 4 calls I think" wayan tajujjuya takalla dan ko kadan bataji ringing ba ahankali tace "banji ringing ba" hannunshi yamika mata yace "let's see maybe kintaba wani waje ne" bashi wayan tayi yakarba yabude ganin ba key saikuma ya kalleta yace "bari zan miki setting nashi anjima wayan nason update, yanzu dai our Boss yazo he's in his office, maisa kikai latti, our Boss is such a wired dude fa" yay maganan kaman mai whispering din gulma da hakan ma yasa tai murmushi, tsayawa yayi yana kallonta yace "instead of kifara tsoro kinyi latti murmushi kike ko zaiyi deducting a salary ki sanan yau saikin biya bashi time din dakikaci by adding extra hours kan lokacin tashinki, oya let's get going" yay maganan yana tafiya tana biyedashi abaya yace "zai miki tambaya, so yanzu idan kinje as normal yanda any boss zaiyi he will ask u few questions ma sababbin staff nashi, yadan miki tambaya karkiji tsoro be very bold and answer him kinji" gyadamaikai tayi suna hawa stairs, yace "and idan yace maisa kikai latti me zakice? Uhmmm kuma banaso nakoya miki karya"? yay maganan yana tunani yadaura yatsanshi akai yana tafiya, dasauri tana kallonshi itama tana tafiya tace "zance mai nakone akafa" kwalalo idanu yayi ya tsaya yana kallonta, gyadamai kai tayi kaman wata yar yarinya tace "wlh dazu nadebo ruwan tea shine yazube akafana yay zafi sosai saisa nai latti" tunda take maganan yake kallonta saida tagama ahankali calmly yace "kinyi kuka"? Gyadamai kai tayi da zuciya daya tana raurau da idanu tana tafiya, chak yatsaya heart dinshi nawani irin racing he feels kaman yajawota ya rungumeta ya lallasheta, jin shiru yasa tawaigo ganinshi abayanta yasa tadan zaro ido tace "menene, ka manta dawani abu ne" dan murmushi yayi yataho da saurinshi yace "no, how's the leg now? Yadena zafi?" gyadamai kai tayi tace " yadena" daidai nan sukakai 5th floor, tsayawa yayi daganan yace "our Boss is a bit harsh but don't get scared okay" gyadamai kai tayi tanadan zaro manyan idanunta, dan yatsine fuska yayi yace "naaaay! I don't like that face, now smile and go you got this" 👍 yamata thumbs up da hannu dayasa tai murmushi sanan tawuce tafara tafiya mutanen dake wajen sai kallonta suke, gaban office dinshi da aka rubuta CEO taje ta tsaya, ga secretary dinshi awajen zaune gaban table tana aiki, ganin ta tsaya yasa tace "you can go in Mrs Du'a" gyadamata kai tayi batare datai magana ba sanan ahankali tadaura hannunta kan handle na kofan harwani kalan sanyi takeji sanan gently tabude kofan kanta akasa, wani irin kamshi da sanyi ne suka wani daki fuskanta dayasa tadan lumshe ido kadan sanan tabude idon kafin ahankali tasa kafanta tashigo sanan tamaida kofan tarufe ta jingina da kofan kanta akasa still hannunta duka biyun kan hannun handbag dinta data kankame gam gam tanajin wani irin sanyi tundaga kafanta har tsakiyan kanta dan sanyin office din yabaci kaman ankure AC gabaki, takai kusan 1min tsaye awurin tana kankame da igiyan handbag dinta kaman her whole life depend on it sanan ta daure still kanta akasa kaman wata munafuka tashigo har zuwa gaban hadadden table din office din ta tsaya gaban kujeran guest tana kara kankame hannun jakan tama rasa takamaimen mezatace a office din mai kamfanin nan, tunawa da maganan Sharif na kartaji tsoron yasa tahadiye tsoron ahankali tabude bakinta cikin muryanta data kara wani irin kankancewa sabida yanda ke faduwa tace "good morning Sir" takai kusan 30sec dagaidashi jin shiru yasa gently kaman wacce idanunta ke shirin fitowa sabida tsabagen rawan dasukeyi tadago kanta takalli kujeran zaman mai office, ido hudu sukayi da Asad dake zaune yana yasanya wani hadadden Italian suit white da blue, wanda keda wani monkey jacket da farin riga ke kasanshi, babu jacket ajikinshi ya rataya kan maratayan da ake ijiyewa a office dan hanging kaya monkey jacket da farin riganne kawai ajikinshi yana zaune kan kujeranshi hannunshi rikeda wasu papers dayake reviewing ga coffee agabanshi yana sipping, sai dayan hannunshi rikeda byro ko kallonta baiyiba, wani irin rawa jikinta yafara ganin Asad mutumin daya cirota daga rijiya a kano, mutumin data gani a TV, mutumin datagani a hotel hall, same mutumin da dazun nan taganshi agidansu shine kuma still take gani anan shine mai kampanin nan, the CEO boss dinta to kodai aljani ne, jitayi cikinta yawani irin murda kawai taji wani fitsari yataso mata yacika mata mara yana shirin zubowa duka acikin yan sakannin data dago kanta ta kalleshi, daurewa tayi ta harde kafafunta gam but still jikinta rawa yake takara kankame jikinta, saida yagama reviewing document din hannunshi yay signing tsaf sanan ya yunkuro ya ijiye papers din kan table sanan ya gyara zama da kyau ahankali yadago kanshi yazuba mata mayun idanunshi akanta, dawani irin sauri tadauke kanta tana kallon gefe tana kara harde kafanta sabida wani irin fitsari datakeji dake neman fin karfinta, cikin muryan nan nashi dababu alamun wasa cikinshi yace "kinyi latti awa daya da minti biyar da sakan lalatin, bayan kinzo aiki latti kika tsaya kina chatting da wani ma'aikaci anan did you know the gravity of laifin nan"? gizgiza mai kai tayi still kanta na kallon gefe, tsawa yadaka mata yace "nobody answers me with motion speak up" wanan karan batasan lokacin data saki hannayenta dake kan jakaba takai tadaura Ata wajajen abdomen dinta dan tana neman sakin fitsarin sosai, lips dinta narawa sosai tace "I am sorry sir......." yana kallonta still yace "well your salary will tell u if I accept the sorry or not, have a sit" gyadamai kai tayi saikuma da sauri tace "okay" kafin ahankali tasa hannunta taja kujeran gaban table din tazauna jikinta na bari. Anatse yace "look up and introduce yourself" yay maganan bayabo ba fallasa as usual, gently tadago idanunta tadaura akanshi kaman yanda shima yake kallonta, kasa jure kalan idanun dayake dashi tayi hakan yasa tana kallonshi ne amman tadan karkata kwayan idanunta gefe sanan ahankali tace "My name is Du'a, I am 21yrs old, an haifeni a kano, Babana nada mata biyu awajen Mama na I am the first child, nayi school from nursery zuwa JSS 2 a makarantan Royal, that's were I stopped a school". 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR Free page EPISODE 3️⃣0️⃣ Tai maganan tanadan moving da jikinta sabida yanda cinyanta ke rawa tanajin fitsari, jin shiru yasa kaman wata barauniya tadawo da idanunta back saitinshi hada idanu sukayi yana kallonta har lokacin wanan karan kasa rike fitsarin tayi batasan lokacin datawani zabura tamike kaman mahaukaciya ba tana yarfe hannunta dayan hannun kuma takai wajen abdomen dinta tadan kalleshi tana rawa rawa tace "I.....wan......pee...." bamata karasa maganan ba jin fitsarin yazo tasa tawani saki handbag dinta datake rikedashi kan table dinshi kayan ciki duka suka zubo kan table dinshi sanan tawani kwasa a guje tai kofan kofanshi tabude tafice dagudu..... Wani mugun tsaki yasaki yanabin table din nashi da kallo da kayan cikin jakanta dasuka zubo, the first thing da idanunshi suka sauka akai was pad, dauke kanshi yayi yay tsaki, yana kokarin dauka wayanshi aka bude kofan aka shigo itane kanta akasa, maida kofan tayi ahankali tarufe sanan takaraso har gaban table din, ganin yanda kayan jakanta suka fito kan table din yasa tadan kalleshi ganin yana daddanna wayan yasa takwashe dasauri tazuba a jakan sanan tadaga jakan tarike kaman wacce zatai sata ta lallaba tazauna akan table din. Ijye wayan dayake tabawa yayi tadau wani file yabude batare daya kalleta ba yace "I learned that HR dept basu karbi any of your detailed ba ID Card na this company kawai MD yasa amiki" gyadamai kai tayi kanta akasa tace "yes sir" still yana duba rubuce ruvuce yace "can I have ur personal ID Card?" dan dagokai tayi takalleshi hada ido suka sakeyi dasauri ta girgizamai kai tace "uhm bandashi" danjim kafin cikin wanan muryan nashi yace "voters card or national identity card dinki that's what I mean" sake dago idanunta tayi takalleshi ganin yana kallonta still yasa tadauke kai murya chan kasa kaman wacce ke tsoro tace "bandasu" cikeda haushi yace "what nonsense! Are you even a Nigerian citizen"? Yay maganan da fushi cikeda kuma fada, doguwan riganta takama tarike gam tawajajen cinya batasan maisa ba fada ko magana da ita da fushi sosai yana tuna mata da memory na gidansu, kuka ne taji yazo mata tadaure da kyar tace "ba....ba'a barina fita agidane saisa bandasu" tai karashe maganan tanakai bayan hannunta kan idanunta tana danne hawayen dake shirin zubomata tanajan hanci, Yatsine fuska yayi kaman irin dan dole yake mata magana dinan yace "give me ur account details we need to attache it to your file for ur salary pension, Sigma pension zasuzo subude miki pension account dinki, now ur bank details" dan dago kanta tayi takalleshi idanunta sunyi ja, hada ido sukayi dan har lokacin kallonta yake murya chan kasa tace "I don't have an account" goshhhh! yawani irin buga table din dayake kai dasaida tama firgita, cikeda bacin rai yace "what kind of a girl Ammi tasa nakawo into my company eh? How can I hire a person who doesn't have any identity card dazai nuna she's a Nigerian and a citizen, please get out of my office, and don't come back to this company saikin bude account sanan kinsami ID card, understood?" Gyadamai kai tayi ahankali hawaye yacika mata idanu fall, yatsine fuska yayi yace "now get out of here" ahankali ta tashi jikinta har bari yake irin na wanda ke shirin yin kukan nan, dawani irin sauri sauri tafita daga office din nashi tai stairs dasauri sauri take sauka kasa kanta akasa ta daure iya daurewa karta bari tai kuka tana kaiwa kasa tai hanyar fita, receptionist dinsu nabinta da kallo cikeda mamaki dan tasan kullum wanan yarinyar da duk suke kirada Matar MD Sharif ta shigo bata sake fita sia lokacin tashi. Tana fita tai hanyar parking space, sai alokacin tafashe da kuka sosai ganin babu motar direban Grandma yasa ta tuna lokacin tashi baiyiba, ga wayanta bayama hannunta yana hannun Sharif dawani irin gudu tafita tana kuka sosai tana share fuskarta da bayan hannunta, bakin titi ta tsaya tana kalle kalle. Idanunta sunyi jajir takasa daina kuka, taxi dayazo wucewa ta tare dan bataga keke napep ba kaman yanda lokacin nan kafin asa tadaina fita take gani akan titinsu, tsayawa yayi ba bahaushe bane yakalleta tsayarda hawayen tayi tashiga sanan tarufe yace "madam ba drop u want" gyadamai kai tayi tace "eh" sosai take kuka cikin keken kawai memory gidansu dakomi yake dawomata da yanda yawani korata kaman yana koran kare, jin yanda take kuka yasa mai taxi yakalleta ta cikin mirror yace "hope all is well o Madam, u no tell me where I go carry you go" murya chan kasa cikin kuka sosai dan daura hannayenta tayi akan fuskanta tana kukan tace "estate" dasauri yace "which estate" kasa amsashi tayi sabida kuka hakan yasa yace "eh which estate" ko kadan batasan sunan estate dinsu ba bama hakaba ita bamatasan ko estate din nada suna ba dan bata taba luraba ahankali tace "just go if we get there I will show you" gyadamai kai mai taxi yayi daba bahaushe ba yacigaba da sharara gudu tana kuka hardaga baya ta lallashi kanta tai shiru tajuya tana kallon hanya ganin bataga estate dinsu ba, sunyi tafiya fin awa biyu suna zagaye zagaye yana tambayanta duk wani estate dazasu gani a hanya konasu ne tace a'a, gajiya yayi yay parking akan wani titi cikin fushi yace "abeg give me my money and leave my car u donno where u dey go" girgizamai kai tayi cikin muryanta data dishashe tace "I know is estate, idan akabi titi ake kaiwa" tsayawa yayi baki bude yana kallonta ta glass din motar ganin kaman ma yarinyar batada hankali dan inba hakaba tayaya babban mace haka zata wani cemai idan akabi titi ne za'azo estate dinsu batasan ina zata bane, harzuka yayi yace "just give me my money find another taxi, the little petrol wey remain make i manage am go home" kalan titi dasuke tayi dababu ma mutane sosai babu motoci sosai dan irin titin sabuwar hanya dinan ne yasa cikeda tsoro tace "but this is not my estate, I don't know anybody here" cikeda nakan magana yace "me I no, see Madam gimme my money comot for my car" ganin yana magana kaman zai daketa yasa tashiga bude jakanta, she's not even sure kotanada kudi, kudaden dake cikin jakan taciro hakan yasa yace "my money na 5000, na drop u carry we almost round Abuja finish" gyadamai kai tayi tashiga kirga kudin jakan duka duka 4900 nema, ahankali tamikamai ganin baida mutunci tace "is 4900 sorry" fizgan kudin yayi yace "witch even if na send they send u my papa spirit still dey protect me, comot for my car" yay maganan yana wani irin bude kofa yafita yabude baya yana kallonta yace "I said comot for my car" fitowa tayi ahankali tana gyara rikon jakanta maida kofan yayi yarufe sanan yakoma gaba yazauna yarufe kofan lekowa tayi ta window yace "I pass ur power tell them u no fit do me anything witch" yay maganan yanajan mota shi duk kallon mayya yakema Du'a sabida yanda takeda bala'in kyau gashi tagama zagaye Abuja dashi zarginshi shine zatakaishi ashamai jini ne. Hawaye tagoge daga fuskanta da sauri bayau aka saba kiranta da mayya ba, ahankali takalli gabas, kudu yamma da arewa tana tunani inane hanyan zuwa gidansu, gashi babu wasu mutane a hanya sosai, hakan yasa ta yanke shawaran bin hanyar da mai motan yabi da kafa, dan batada ragowan kudi kuma koma tanada shi bataga taxi ko keke napep dazata tare anan ba ga cikinta dayake ciwo dan bataci abinci ba gakuma MP datakeyi datakejin alamun na yakamata ta chanza pad dan kaman yajike. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR LAST FREE PAGE EPISODE 3️⃣1️⃣ Sosai take tafiya Instead of taga tana shigowa cikin mutane amman saitaga kaman tana kara komawa inda ba mutane ne, one one motoci ke gittawa, tun wuraren 1 da direban nan yasauketa itace har uku saura tafiya take kafanta yay budu budu sabida a bayanta dakejan kasa ga shegen kishin dayakeji ga yunwa ga gajiya, tsayawa tayi abakin titi duk motan dazaizo yawuce take tarewa amman basa tsayawa hakan yasa takoma gefen titi dan daji da bishiyoyin dake wajen tasamu ahankali tazauna akan wani dan dutse dake wajen tana maida ijiyan zuciya tanajin wani shegen kishi tana kalle kalle bataga komiba, daura jakanta tayi akan kafafunta kafin ahankali tadaura kanta akan jakan kawai tafashe dakuka ahaka akife kafin daga bisani wani wahalallen bacci yay awon gaba da ita awajen. Wuraren 1 as usual Sharif yazo floor dinsu rikeda wayanta daya saita mata komi, knocking office dinta yayi tareda budewa duka at the same time, ganin babu kowa a office din babu jakanta yasa yadanyi kwafa yace "yauma ta tafi masallacin bata jirani ba ko" jan kofan yayi yamaida yarufe yafito daidai Asad yadawo shima daga mosque din yana tafiya ahankali yana gyara zaman necktie dinshi yana kallon Sharif din, tsayawa kusadashi Sharif yayi cikeda tsokana yace "how far kamana order pizzan" hararan Sharif din yayi yace " order with ur money" yay maganan yana wucewa office abinshi shikuma Sharif yahau dariya yawuce elevator yashiga zuwa kasa masallaci yashiga yay alwala yay salla sanan yafito yana kallon wajen ganin babu ita yasa yawuce Canteen dinsu, ganin babu ita awajen ma yasa yay fushi kawai baima tsaya cin abincin ba yawuce floor dinsu yace "nizata share yau duk tai abubuwan ta ita kadai" wayanta ya kalla dake hannunshi yace "she will come get it by her self" ijiye wayan yayi agefe kan table dinshi yacigaba da aikinshi...... Wuraren 3 yakasa hakuri rabon daya ganta tun safe tashi yayi yafito yay sama, office dinta yasake budewa ganin bata ciki yasa yafito yabi ma'aikatan wajen da kallo wucewa yayi yakarasa wajen receptionist din gaban office din Asad yace "have u seen Miss Du'a Patience"? Cikeda girmamawa tace "yes sir naga saukanta" juyawa yayi da sauri yashiga elevator yasauka kasa, shi yasan bata yawo iya kanta masallaci sai Canteen kuma duk tare suke zuwa toko tana restroom din mata ne, hanyar bayi yayi ya tsaya gaban macen security dake wajen yace "dan dubamin miss Du'a aciki" tashi matan tayi tac3 yes sir tashiga taduba tafito tace "babu kowa a rest room sir" shiru yayi yana tunani dan this is strange, daga kai yayi yana kalle kalle ganin receptionist din wajen yasa yakarasa yace "have u seen Miss Du'a"? Gyadamai kai tayi tace "yes Sir dazu naga tazo tawuce tafita tana kaman ma kuka take" dan tsayawa yayi yana kallonta saikuma chan yace "around what time kenan"? Dan shiru tayi kaman tana tunani tace "around eleven na safe" juyawa yayi dasauri cikin fushi yace "Assssadd! What have u done this time" elevator yahsiga zuwa 5th floor, direct office din Asad yashiga dake magana dawani employee dinsu daya kawonai report, kallon employee Sharif yayi yace "excuse us Mr Bashir" "sure sir" yafadi yana tashi yafita sauda yarufo kofan sanan Sharif yakalli Asad babu alamun wasa kaman bashiba yace "ina Du'a Asad? Inaka turata" dan yatsine fuska Asad yayi yana jawo MacBook dinshi zuwa gabanshi yace "wace Du'a"? Cikin fushi Sharif yace "you know what am talking about, yarinyar dakai saving daga rijiya, jikan Hajiya, yarinyar da Ammi tasa kabata aiki, ina take"? Typing abu yashigayi a system dinshi abinci cikin halin I don't care yace "batada any means of identity sanan batada account so I asked her to leave my company duk randa tasamesu she can come back" cikin wani irin bala'in mamaki Sharif yace "you ask her to mene?" yay shiru yana kallon Asad dake harkan gabanshi, cikin wani irin bacin rai yace "Asad kakosan mekayi? Did you know that yarinyar nan batasan ko'ina ba a Abuja ko good 3weeks batayi a Abujan nan ba, tayaya zata koma gida? Look her phone is with me" yanuna wayanta dake hannunshi, dan tabe baki Asad yayi yana aikin dayakeyi a system yace "she's an adult she can take herself home" yanda yake maganan ma yafi komi cima Sharif rai irin ko ajikinshi dinan baimasan yayi wani abuba, cikin mugun fushi dabazai iya tuna the last time dayay irinshi ba yace "wlh katashi kanemo yarinyar nan ina gayama" wanan karan ko kalloma Sharif bai isheshi ba saima hannunshi dayakai yana taba screen din system din yana magana ahankali yace "there's an error in this FIFO calculation......" irin baimasan Sharif nayiba, sosai ran Sharif yabaci wayanshi yaciro ya danna ma Ammi kira yadaura a kunne ringing biyu Ammi tadaga kafinma tai magana yace "Ammi kina ina yanzu haka" cikeda rashin fahimtan abinda Sharif keyi tace "ganinan gidan Hajiya, takirani gwuiwanta naciwo shine na shigo" ahankali yace "Ammi Du'a na gidan" dasauri tace "Du'a kuma, Du'a dake office basai 4 kuke tashi ba, wai yau bakaje office bane" wani irin lumshe ido yayi yabude kirjinshi na bugawa yace "Ammi listen to me zangaya miki wani magana amman banson kice komi dan kar Hajiya tagane dan abinda kunya ace mune mukama jikanta haka" nan yakorama Ammi magana daga A to Z, tsabagen tashin hankali batasan lokacin data fito tsakar gida ba, cikin bala'in bacinrai tace "ina Asad din"? cikin bacinrai Sharif yace "yana zaune anan Ammi ko ajikinshi baimasan yayi abu" cikin fushi sosai tace "bashi wayan" cikin bacin rai yace "ni wlh bazan bashi wayataba saidai ki kirashi ta wayanshi bari naje naduba Nabi hanya kozan ganta" yay maganan yana katse wayan yawuce yafice daga office din straight waje yayi yashiga motanshi yabi hanya. Wayan Ammi tabida kallo tunda take bata tabajin Sharif yayi fushi hakaba duk cikin yaran shi kadaine baida matsala gashida ban dariya, dialing number Asad tayi, yana zaune ganin Ammi na kiranshi yasa yature system din dake gabanshi yana kallon wayan harta katse bai daukaba, akaro nabiyu ne yamika hannunshi kaman mai tsoron wayan yadauka yakara a kunne baice komiba, cikin fushi sosai Ammi tace "aida itama wanan kiran baka dauka ba goga kaji" taidan shiru hakan yasa ahankali yace "Ammi I just told her to go idan tai national ID da bank saita da......""shut up Asad!" Ammi tadakamai mugun tsawan dashi zai iyacewaka tunda yake arayuwanshi Ammi bata tabamai tsawa hakaba, tace "Asad this is not how I train u wlh billahil azim, Asad where is your heart, Asad how can u asked that girl ta tafi gida yarinyar dabatasan ko'ina ba, kasan yarinyar nan kuwa? Kasan wacece ita? Eh? kasan mesa aka kawota wajen kakanta kasan labarin Du'a kuwa? Do you know what that girl has been through? Asad is this how I trained you? Duk duniyan nan banda Maman data wuce Hajiya Asad you know this morethan anyone matan nan babu abinda batamin ba aduniyan nan, Asad jikan ta zaka wulakanta eh?" jin yanda ran Ammin shi yabaci sai maganganu take awaya yasa yaji duk badadi, ahankali yace "Ammi" cikin fushi tace "don't you dare call me Asad, idan wani abu yasami yarinyar nan tayaya zankalli Hajiya nagayamata d'ane sila eh? Mezata cema iyayen yarinyar nan kasan case din dake kan yarinyar nan kuwa, Asad why are u like this? Maisa baka da imani bakada tausayin mata eh? kanada kannai mata idan wani yakorasu haka kaibamai zuwa kayi fada dashi bane, Asad listen to me if anything should happen to that girl wlh wlh bazan yafemaka ba dan bazan taba iya kara kallon idanun Hajiya ba..." dawani irin sauri yace "Ammi!" cikin fushi tace "yes Asad nasan kalman dana gayamaka, katashi duk inda yarinyar nan tashiga aduniya ka nemota kadawo da ita gida nan dakanka safe and sound inba hakaba wlh saina mugun sabamaka Asad dabazaka gane kaina ba mai bakin hali kawai" Ammi ta katse wayanta cikeda bacin rai tana kallon agogo dan tasan hudu nayi direban Hajiya zaitafi daukota. TOH GGM DINA🥰🥰🥰 ANAN NAKAWO KARSHEN FREE PAGES THIS LABARI NADA TSAYI YANZU NAMA FARA. SUBSCRIPTION IS 500 PAY INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK. KUJI TSORON ALLAH KUBIYA KADA KU KARANTA BATARE DAKUN BIYABA DAN GASKIYA ALLAH ZAI SAKAMIN. THANK YOU ❤ Assalamu Alaykum, inaso mu gina al'umma masu tsoron Allah da tsoron hakkin dan uwanshi musulmi, I was very kind and generous nayi pages talatin da daya (31) pages awanan littafin as free, dan Allah kudubi Allah badan niba badan halina ba karku karanta idan baki biya kin shiga group ba, dan idan kikai gaskiya Allah zai bimin hakkina. Kudin karatun this novel is 500 kacal, pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting. you can chat me up directly a watsapp by clicking on this link wa.me/+2347012181461 M SHAKUR EPISODE 3️⃣2️⃣ Kasa komawa cikin gidan tayi hankalinta yawani tashi gabaki daya number Sharif tai dialing ringing daya yadaga, cikeda damuwa tace "Sharif kafita nemantan kaganta"? Cikeda damuwa yana driving yace "Ammi ni banmasan ina zan dubaba gani nan dai akan titi within office dai ina dudddubawa" cikeda damuwa tace "shikenan In sha Allah nothing will happen to that girl In sha Allah, now inaso ka kira Hajiya kacemata Du'a will stay late akwai aiki zaku dawo da ita anjima, Sharif kunyan gayama Hajiya abinda d'ana yama jikan ta nake wlh just do that okay" ahankali yace "Ammi calm down Hajiya taganki ahaka zama ta zargi wani abu, kitafi gida kawai and relax we will bring Du'a back, nothing will happen to her kinji" asanyaye tace "Allah yamaka albarka Sharif" takatse wayan. Yadade zaune kan table dinshi yana maimaita kalaman da Ammin shi takirashi dashi, yau Ammi ce ke cewa bazata yafemai ba, Ammi ce kecemai mai bakar zuciya, Ammi bata tabamai fada hakaba, ahankali ya fuzarda iska yamika hannayenshi da kyar yature system din gabanshi sanan yawani irin kife kanshi akan table, kaman wanda aka daka, saida yaji ana kiran sallan laasar sanan yatashi, mikewa tsaye yayi yashiga bathroom dinshi dake cikin office din, alwala yadauro sanan yafito ya tsaya gaban hanger jacket na suit dinshi yasaka sanan yadauki wayanshi da car key daga wajen yawuce fita yayi yasauka kasa saida yafara tsayawa yay sallan laasar sanan yafito daga masallacin tsayawa yayi yana kallon entrance door din shigowa company, shi yanzu ta ina Ammi takeso yafara neman yarinyar nan me eh ta ina?. Ahankali yafara tafiya zuwa entrance din fita yayi yawuce special wajen dayake parking motarshi, budewa yayi yashiga yamaida kofan yarufe ahankali yasake fuzarda iska, wani irin tsaki yayi sanan takunna motarshi yaja saiya yakai daidai titi ya tsaya yana tunani, yasan estate dinsu babu suna agate wani irin mahaukacin estate ne na masu kudi saisa settings dinshi ma daban ne dana sauran estate, in shine ita baisan ko'ina agarin nanba yana tare abin hawa cemai zaiyi yakaishi estate, so now dole yabi hanyoyin all estate na within this yanki haka, tsaki yakara ja kaman yahadiyi zuciya sabida haushi yaja motar dawani irin mugun gudu yanabin hanya hanya estate estate yana duba kozai ganta amman har magrib baiganta ba at this point he was a bit worried bawai dan wani abu ba kawai sabida Ammi da kalamanta da fadan datamai, kuma yasan inda anganta da yanzu koda Sharif ne daya sanardashi anganta, ahankali yay parking yafito ya tsaya awani masallaci yay alwala sanan yay sallan magrib yasake fitowa yashiga mota yaja yana gudu akan titi yama dauki hanyan barin gari wani irin dukan sitarin mota yayi yana tsaki, saikuma yadagokai yadaura akan titi gani yayi kaman yawuce wani abu haka a gefen hanya dawani irin sauri ya leka ta side glass yana kallo maiya hango baya hango kaiko kafa kawai kaman abu yagani ciki ja da bakin kaya, murya chan kasa yace "can that thing be the girl"? Yay maganan ahankali yanayo reverse da motan ahankali harya tsaya daidai saitin ta yana kallonta daga wajen yar jakanta dake kasa agabanta dayagani yasa ya tabbatar da itace, dawani irin sauri yasaukar da glass din motar kasa yaleko da kanshi tareda danna horn, amman ko alamun motsi baiga tayiba, sake danna horn yayi sosai but still babu ko motsi, sosai ranshi yabaci shiyake yar yarinyar nan da duka kannenshi sun girmeta horn ne ta shareshi, wlh sabida maganganun Ammi ne daya rantse yaja mota abinshi yay tafiyanshi ita tasani, cikeda fushi yace "ke kitaso nakaiki gida" ganin har lokacin ko motsi batayi ba yasa yadanji gabanshi yafadi, dan jim yayi yana tunani saikuma yabude kofar motan yafito ya tsallaka dan kwatan gefen titi sanan yakaraso wajen dajin yana yatsine fuska ga uban kukan sauro dayake duhu yasomayi, akanta ya tsaya yana kallonta cikin muryan dolen nan aka tirsasashi yay magana yace "Ke bakiji ana kiranki bane, tashi muje nakaiki gida" jin shiru still ko gezau batayi yasa yaciro wayanshi daga aljihu dasauri kunna flash yayi ya hasketa baya ganin fuskanta sabida yanda takife fuskan kan kafafunta, bayanta ya tsare da ido yana kokarin detecting breath nata ganin baiga sign na numfashi ba yasa dasauri ya tsugunna agabanta ijiye wayanshi yayi agefe yakai hannunshi zai tabata saikuma ya tsaya kallon hannunshi yayi dasauri saikuma yakai duka biyun yadaura daya kan kafadarta yay tapping nata yace "Ke, Ke" ganin still ba response yasa yazare hannu daya daga kafadarta yakai dayan saman kanta dago kanta yayi sama hakan yasa dankwalinta gabaki daya ya salube kanta na resting a hannunshi, sauke dayan hannunshi dakekan kafadanta yayi yadauki wayanshi da sauri yana haska fuskanta, kumburin da idanunta sukayi saida yaji tsoro tsabagen kukan datasha, idanunta abude amman kadan tana kallon flash din wutan dake haskota, lips dinta sun mugun mugun bushi kaman zasu tsage tsabagen rashin ruwa dakuma rana ga uban iskan hanyan daya bugeta, juya flash din yayi akan fuskanta dan yaga ko she's conscious, ahankali yaga idanunta sunbi flash din, hakan yasa ya ijiye flash din yakai hannunshi yay tapping kumatunta yace "Ke....Ke....Du'a!" bakinta yaga yay motsi hakan yasa dasauri yakai kunnenshi saitin bakinta, ahankali yaji tafurta ru.....bata iya fura sauran ba, dasauri yasaketa yatashi motanshi yakoma wani bottle water dayakedashi yadauko yadawo dasauri yasake tsugunnawa yabude yakai hannunshi daya yadaura saman kalban kanta sanan yakai ruwan bakinta dawani irin sauri tashiga shan ruwan dakawai saiyaji he's feeling bad, katon bottle water nan saida ta shanye tass dazai karamata wani ma yasan dazata shanye, yarda goran yayi yakalleta sai alokacin idanunta suka budu da kyau, ahankali tazubamai nata idanun sabida wayanshi dake kasa they could see each other, tundaga gashin dasuka kwanta akan goshinta yake kallo zuwa gashin idanunta bakake sidik dogaye dasuka tattare sabida uban kukan datayi, zuwa manyan idanunta dasuka kumbura suntum idanunta sukai kanana kaman na yan Chinese sabida kuka, zuwa dogon hancinta dayake nan akan fuskanta tsaf zuwa sexy a little bit thick and slim towel lips dinta dakenan atattare tsukakke pink yirrrr dasu sun buce sosai sabida wahalan datashi, dan kawarda kanshi gefe yayi dasauri kaman wanda yatuna wani abu, wayanshi yadauka yatura a aljihun wandonshi sanan yacire hannunshi daga saman kanta yamike tsaye yace "tashi mutafi" ahankali tai kokarin tashi ta hanyar rike bishiyan dake side dinta tamike tsaye, ganin haka yasa yawuce yay gaba abinshi, gently tacire hannunta daga jikin bishiyan batasan meya faruba kawai tajita tazube a kasan wajenne kaman wacce kafafunta sukai paralyze. Haryakai mota yana shirin shiga yaji karan fadin abu dawani irin sauri yajuyo ganinta akasa still tana yunkurin tashi zaune ne dankwalinta gabaki dayama yacire yasada wani irin sauri yazo wajen, kamota yayi ya tsayarda ita jin kaman lema lema ajikinta yasa dasauri yasake saka hannu a aljihu yaciro wayanshi da flash din yake a kunne yahaska jikinta, ganin stain a riganta dudda baki da jane bai hanashi gane stain din jini bane, kallon fuskanta yayi yanda bamata iya bude idanu da kyau da support dinshi ma ta tsaya yasa kawai yamaida wayan aljihu, ahankali yacire jacket din suit dinshi, yatsine fuska yayi yadan matsoda ita yasata ajikinshi gudun karta sake faduwa dan yaga jiri take gani sosai, kaman jira take dawani irin sauri ta kankameshi gam gam tana tura kanta a kirjinshi tana nishi sama sama wani irin yunwa nacin cikinta kaman zata suma takeji, wani irin yirrrr yaji yanda gabaki dayanta take cikin jikinshi gashi ta kankameshi sosai, ahankali yakai jacket dinshi yasamata Ata wajen waist dinta sanan yakamo hannaye jacket din yazo dasu ta gefenta yarike sanan yafara tafiya da ita ahankali tana rungume dashi da sukazo wajen kwata daukanta yayi ya talla kar da ita sanan yabude gaba yazaunarda ita, dan dukowa yayi yana samata sit belt yana kallonta yanda ta lumshe ido ganin kanta ba dankwali yasa maida kofan motan yarufe sanan yawuce we amen dankwalinta yadauko sanan yadawo yashiga gaba ya zauna yatada motan yaja motan da bala'in gudu. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR Assalamu Alaykum, inaso mu gina al'umma masu tsoron Allah da tsoron hakkin dan uwanshi musulmi, I was very kind and generous nayi pages talatin da daya (31) pages awanan littafin as free, dan Allah kudubi Allah badan niba badan halina ba karku karanta idan baki biya kin shiga group ba, dan idan kikai gaskiya Allah zai bimin hakkina. Kudin karatun this novel is 500 kacal, pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting. you can chat me up directly a watsapp by clicking on this link wa.me/+2347012181461 EPISODE 3️⃣3️⃣ Sosai yake gudu yake kallonta yanda ta lumshe ido tana numfashi sama sama kaman ma bacci take, wayanshi dayahau ringing yakalka ganin Ammi ce yasa yamika hannu ahankali yadauka kafinma tai magana yace "I've seen her Ammi muna hanyan zuwa" ya katse wayan kafin tagayamai wani maganan, gaban wani eatry ya tsaya kashe motan yayi yakara juyawa yakalleta bayawani ganin fuskanta sosai sabida tajuya tana facing kofa tana bacci gashinta kawai yake iya gani da ribon din yafita kitson ya zuzzuba ajikinta, bude kofa yayi yafita yashiga eatry youghurt yasayo mata da jellof rice da roasted chicken sanan yafito, zagayawa yayi ta bangarenta yabude kofan fuskanta ya kalla taga da kyar take bude idanu, yogurt din yaciro daga leda yabude marfin yabata yace "Ke gashi ki sha" kallonshi take takasa ma mika hannu ta karba ko kadan batada karfi, ahankali tadanyi shifting hannunta zata mika ta amsa amman takasa, sosai yaji gabanshi nafaduwa yamaida yarinyar ahaka ai sai Ammi takusan kasheshi da masifa, dan tsaki yasakeja na mugun takaici sanan yabude marfin goran yogurt din yadanyi bending yakai kan bakinta wani irin zuman goran tayi tanasha sai lokacin wani karfi yazo mata batasan lokacin datakai duka both hannayenta tadaura kan nashi dake kan goran takara kankame goran da hannunshi tanasha sosai, wani yar yaji yadai daure ganin tana neman ta shanye yogurt din yasa yafizge goran yana kabar da hannunta yamaida goran yarufe ya ijiye sanan yabude take away abincin yadaura kan cinyanta yace "eat" sanan yamaida kofan yarufe yana zagayawa yanadan dunkule hannayenshi yana budewa jin warmth na tafukan hannunta haryanzu akan nashi, bude kofa yayi yashiga sanan yatada motan yaja batare daya kalletaba tafiya kadan yayi ya tsaya awani pharmacy shiga yayi yadan jina kadan aciki saichan gashi yafito yazo ta side dinta, bude marfin motan yayi yana kallonta idanunta biyu yanzu sundan bude ga abincin daya ijiye kan cinyanta yanda ya ijiye haka suke, hannu yasa yadauke abincin ya ijiye sanan yabude ledan magungunan dayasiyo, syringe yaciro yana budewa sanan ya karya kwalban alluran daya ciro kafin yasa aciki yazuko allura ita kawai kallonshi take dan ko kadan batada karfin ko magana ba, tsugunna wa yayi yaciro wayanshi ya kunna flash sanan yamika hannunshi kaman bayaso yawani kamo hannunta, dan yunkuri tayi dadan karfin daya zomata zata fizge hannun wani irin mugun kallo yamata yace "wlh in baki natsu ba saina chak miki alluran nan awuya in barar dake awajen nan inyi gaba" gyadamai kai tayi ahankali tana juyarda kanta tanajin kuka na zuwan mata, hannun abayanta yaja zuwa sama ya saiti jijiyanta yamata alluran akai, ko kadan bataji zafiba saiwani sanyi dataji ajikinta har kwakwalwa, tashi yayi ya yarda komi a kwaran wajen sanan yashigo mota yaja, lumshe idanunta tayi jin sanyin datakeji yay yawa gashi ya kunna AC a motan, saikuma ahankali taji wani karfi na saukanmata ajiki dayasa gently tabude idanunta tana mikarda hannunta dataga yana mikuwan mata freely, gyara zama tayi kaman ba itaba, ahankali tadaga hannunta ta taba gashinta jin babu dankwali yasa tashiga waige waige a gefenshi taga dan kwalin dan kallonshi tayi yanda gabaki dayan hankalinshi kekan tukin dayake yi, dauke kai tayi saikuma ahankali tasake juyowa kaman wata barauniya takalli fuskanshi hasken fitilun motoci nadan haska shi, bakaramin kyau yayiba yay looking different sabida yanda babu jacket ajikinshi sai faran riga, dauke kanta tayi ahankali tamika hannunta dataji yana rawa tadauki dan kwalin sanan tayafa akanta ta juyarda kanta tana kallon hanya, almost 1hr drive yayi sanan suka shigo estate dinsu, agaban gate din gidansu yaga Ammi zaune itada Sharif looking damn worried suna hango motanci suka mike tsaye hakan yasa yay parking agaban gidansu Hajiya su Mami kuma suka karasowa wajen da sauri, bude kofan motan yayi yafita yanadan waige waige Mami tai kanshi cikeda fushi yayinda Sharif yay side dinta, bude kofan yayi ahankali yadaura idanunshi akanta yanabinta da kallo daga sama zuwa kasa ahankali yace "Du'a why? Bazaki iya zuwa office dina ki sameni ba eh? Why inda ace something happened to you fa daya kikeso nayi dakaina, kinsan how much u mean to me kuwa? I love you so much" yay maganan yana tsugunnawa agaban motan, kallonshi take tunda yake maganan nan, yanda yanuna yadamu da ita he's worried and fuskanshi yanuna yasa kawai taji kuka yazo mata dasauri tasa bakin gyalenta akan idanunta tana sharewa, daidai Ammi datagama wanke Asad ranta abace tazo wajen, ganin Sharif atsugunne ga Du'a na kuka yasa tace "maiya sameta Sharif Asad yamata wani abune kuma"? girgixamata kai yayi yana mikewa tsaye ahankali Ammi takai hannunta takamo Du'a tafito da ita daga motan tana binta da kallo rungumeta tayi tace "Du'a dan Allah kiyakuri kinji" ganin stain a sit din data zauna yasa gabanta nafaduwa taciro Du'a daga jikinta tace "are u on MP ne"? gyadamata kai Du'a tayi tana goge fuskanta tass, Ammi takama hannunta tace "taho muje wajen Hajiya" sanan tajuya takalli Asad dake inda tabarshi kanshi akasa tace "kazo nan kayi bayanin abinda kayima jikanta da bakinka Asad nagayamaka" taja hannun Du'a sukai ciki Sharif biyeda su, rufe motanshi yayi cikeda kunci ya biyo bayansu ya shigo ciki. Da sallama Ammi tabude kofar falo Hajiya na zaune kan kujera tana karanta news, ganin Ammi da Du'a datai butu butu ga jacket daure a wrist dinta idanunta sunyi ja yasa tasauke jaridan dake hannunta takalli Sharif dake tsaye gefensu saikuma ga Asad da tana kallon fuskanshi taga kalan bacin ranshi, juyawa Ammi tayi takalli Asad cikin fushi tace "shigo nan, shigo ciki kayi bayani da bakinka" ahankali yashigo ciki yazo ya tsaya gaban Hajiya daya kasa hada ido da ita kanshi akasa, cikeda masifa Ammi tace "i said talk Asad"! hannu Hajiya tadagama Ammi tace "Zainab yahaka! Ba'a ma Babba fada agaban karami" tajuya takalli Du'a dake tsaye tace "wuce sama kije kiyi wanka ki chanza kaya" gyadama Grandma kai tayi tawuce ahankali saida takai sama sanan Hajiya tajuyo takallesu Sharif takalla tace "Ya akayi Sharif bakacemin Du'a will stay late zaka dawo da itaba, lafiya kuka tasomin d'a haka kunamai ihu aka" tai maganan tana murmushi kaman bata gane komiba, cikin wani irin kunci Ammi tace "Hajiya wanan ne d'a" tanuna Asad da kanshi ke kasa tace "inda yaci d'a dabai wulakanta Du'a haka ba, kinsan meyayi kuwa...." daidai da abu daya Ammi bata boyema Hajiya ba tafadi mata tace "wlh yau Asad na kunyatani" dariya Hajiya tayi tace "yanzu akan wanan ne kika taso yaron nan haka kina humiliating nashi agaban kannenshi Sharif da Du'a haba Zainaba" sake baki Ammi tayi tana kallon Hajiya, juyawa Hajiya tayi takalli Asad ahankali tace "Asad" dago kanshi ahankali yayi cikeda kunya ya kalli Hajiya murmushi tamai tace "thank you Allah yamaka albarka" sanan takalli Ammi tace "wlh wlh Asad baiyi kuskure ko kadan ba, hasalima mai laifin Du'a ne" Hajiya tadanyi shiru tace "nagaya muku sabida Du'a na jikata banso kubata wani special treatment yanda Asad will punish other employees that should apply to Du'a too as well, tambayan means of identity na mutum da bank account is normal procedure dakowani organization keyi, idan batadashi yanada right yacemata tawuce tatafi duk randa tayi tadawo I love that yes! Asad shows leadership skills awajen, laifin Du'a is boss dinta yabata punishment she could have pleaded kan ya yakuri zatayi gobe that's 1, secondly is dataje office din Sharif takarbi wayanta daganan zata iya gayamai shima yay pleading da Asad tazauna, thirdly is kodama yakoretan zata iya hanging around a mosque canteen kowani waje zuwa 4 direban ta yazo yadauketa su koma gida" Hajiya tai murmushi tace "Alhamdulillah I can now say that Du'a tafara girma, this girl spend about 8 zuwa 9yrs indoors ko falo haka ba'a barinta tasauko, tun Du'a na JS2 mahaifinta yay grounding nata, saisa idan ka dauko Du'a kasata cikin age mates dinta zaka gani she's totally different in the sense sunfita wayau sunfita iya da sanin komi, Du'a bata taba experiencing something like this ba, so it's time at 21yrs tasan what is life and what is life all about, thank you Asad, I promise zan kaita tabude bank sanan zamuje tayi national identity card sanan zata dawo" tunda take maganan Ammi ke kallonta harta gama tace "Hajiya yanzu bazaki ma Asad fada ba kan abinda yayi inda tabace fa" cikeda wasa Hajiya tace "idan mutum yay abin fada kinsanni nafi kowa iyama mutum fada but trust me this time Asad baiyi komi ba, and listen what all of you did today dagake Sharif Asad just shows ko bayan raina u all will stand for Du'a and support this my innocent child sanan kutayani training nata, so wlh harga Allah har cikin raina banji haushi ko riki Asad ba rather I am thankful dayake treating nata without sentiment and that's what I want bansan sabida ni aki ayi abinda yakamata" wani irin makirin murmushi Asad yayi kawai yaje yazauna kusada ita ga mamakinsu kawai rungumeta yayi yana murmushi sosai, murya chan kasa batare dasu Ammi sunji ba yace "I am sorry Grandma I didn't know that she will leave the whole building daban korata ba I am not that cruel" murmushi sosai tayi tana kallon Ammi dake kallonsu baki bude, tace "Yaya za'ayi ba'a shiga tsakanina da yaran nan sai hakuri Ammin su" wanan karan dariya Ammi tayi har cikin ranta takeson Hajiya, Hajiya mutum ce wlh she's super duper educated ga iya zama da mutane ga sanin yakamata. Daure fuska Sharif yayi yakaraso yana kallon Grandma yace "Hajiya ni wlh kobazaki mai fadaba ni zanyi duk randa yakara something like this Allah saimun kwashi yan kallo" dariya sosai Hajiya tayi tace "to Oga Sharif tuba Asad yake" lekowa Asad yayi yamai gwalo Sharif yay kwafa, tashi Ammi tayi tana kakkabe jikinta tace "tunda mu aka watsama kasa a idanu bari mu nemi hanyar gidanmu mutafi, kai kuma Asad zamu gamu agida" tawuce Sharif biyeda ita, Ammi takalli Asad tace "Ammin ka tai fushi tashi kabita" gyadamata kai yayi yatashi yafita. Assalamu Alaykum, inaso mu gina al'umma masu tsoron Allah da tsoron hakkin dan uwanshi musulmi, I was very kind and generous nayi pages talatin da daya (31) pages awanan littafin as free, dan Allah kudubi Allah badan niba badan halina ba karku karanta idan baki biya kin shiga group ba, dan idan kikai gaskiya Allah zai bimin hakkina. Kudin karatun this novel is 500 kacal, pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting. you can chat me up directly a watsapp by clicking on this link wa.me/+2347012181461 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 3️⃣4️⃣ Tashi yayi yawuce yafita binsu da kallo Hajiya tayi cikeda murmushi sanan ta tashi dinning taje dakanta batare data kirasu Razika ba tazuba tuwo da miyan kuka da man shanu da nama a plate tawuce sama, bude kofanta tayi ahankali tashiga daidai tana karasa saka riga dan fitowanta daga wanka kenan, akan carpet dinta nakasa Grandma ta zaune tray sanan ta zauna tanuna mata gefenta tace "come and sit" karasowa tayi ahankali tazauna, abincin tanuna mata tace "what stain ur cloth Du'a" Murya chan kasa tace "MP ne bansamu na chanza pad ba" gyadamata kai tayi tace "maisa baki nemi Sharif kin karbi wayanki kin sanardani Asad yakoreki ba" hannu takai jin hawaye yazo mata murya chan kasa tace "kawai dayace I should get out yakoreni abin saiya dawomin da memory gidanmu yanda ake korana sama duk inda naje shine kawai nafita dagudu ina kuk......." saikuma tasake sakin kukan shiru Grandma tayi tana kallon Du'a dan from what she's seeing now Allah ne yaciro yarinyar nan yakawota nan danda depression yakashe Du'a tanada real bad memory of gidansu not good ones, idan ance mata yarda tahaifa Zainab zata iyama yarta haka kokuma zata iya tsayawa tanagani ama yarta haka bazata taba yardaba saisa haryau fada take da Mami, haushinta takeji sabida abinda sukama Du'a, matsarda tray abincin Hajiya tayi ta matsa jawota tayi tasata ajikinta tana bubbuga bayanta sosai tai kukanta takoshi murya chan kasa na lallashi tace "I will say and say this again to you Du'a keda komawa gidan ubanki wlh sai inda karfina yakare kinbar gidan nan har abada, kin barshi kenan so stop crying and leave you life, gobe zamuje mufara yin national Id card akwai wanda nasani zai miki yana fitowa sai mubude bank ko duka duka next week kin fara aiki kinji" gyadamata kai tayi, Grandma tace "good girl, Allah yamiki Albarka kinji" ahankali tace "Ameen" Grandma tace "ina kikaje hope nothing happened to you" girgixa mata kai tayi tace "bansan sunan wajenba mai taxi yakaini babu abinda yasameni yunwa kawai yasa nadinga bacci" dan dariya Grandma tayi tace "Alhamdulillah zokici abinci to maza" da kanta Grandma tasa hannu yashiga feeding yarinyar hakan yasa kuma taci abincin sosai kaman ba Du'a ba, tana gamawa paracetamol tadauko tabata tasha sanan tasa taje tawanke hannu tazo kanta tadaura kan cinyarta tana bata shawarwari kan yanda zatai handling any situation datake ciki ko data shiga ahaka bacci yay awon gabada ita. Washegari!! Hakanan yajima baijin zuwa office yau, kasa fitowa yayi dan jiya kiri kiri kin bin Ammi side dinta yayi yabata hakuri dan fadan dayasha awaya ya isheshi dana kofar gida baison wani kuma a dakinta, ga Sharif yashareshi tun jiyan nan da abin yafaru kodazai tafi aiki ma bai sanardashi ba, sai abin yazo yafara damunshi dan yanason dan uwan shi yasaba every minute Sharif ke tsokananshi yasashi surutu. Wuraren 11 yafito daga side dinsu shima yunwa takadoshi, bude kofan flat dinsu yayi yashiga babu kowa a falon hakan yasa yaji bala'in dadi, dinning yawuce kujera yaja yazauna sanan yazuba shayi a cup yasa chips da egg a plate yanaci, bude kofan kitchen akayi dayasa dasauri yadago kanshi Aneesa ce tana sanye da rigan bacci daya tsayamata a guiwa mai hannun shimi baki, kanta babu dan kwali, wani irin murmushi tayi tace "laaaa Ya Asad bakaje office ba" dauke kanshi yayi daga kallon kofar kitchen din danya dauka Ammi ce batare daya bata amsa ba, dan turo baki tayi aranta tace "shegen wulakanci ne dashi" adan shagwabe tace "Ya Asad good morning" batare daya kalleta ba yace "morning" yacigaba da cin abincin shi, kitchen takoma tajuye Indomie datake dafawa a bowl da egg tadau fork tafito tazo dinning din, kujeran dake facing nashi directly taja tazauna tafaraci, dago kanshi yayi kaman wanda yatuna abu yakalleta ko kadan babu alamun wasa akan fuskanshi yace "why didn't u go to school yau Tuesday"? Dagokai tayi ta kalleshi faduwa gabanta yashiga yi yanda yazuba mata idanu yasa takasa karya ahankali tace "zanje birthday shopping ne birthday dina is this Friday, kuma Mum zatazo daga kano on Thursday" baki yabude zaiyi magana aka bude kofan falo aka shigo hakan yasa duk suka waiga, wani irin ihu Aneesa tayi ta tashi dagudu tai kofan "Daddy oyoyo, Dady oyoyo" tawani irin fada jikin Dad daya shigo yaci bugaggiyar malum malum milk ga gateman biyeda shi rikeda katon akwatin shi gemun nan nashi sai kyalli yake yaji shaving dan yanda tsabagen baison tsufa, budemata hannu yayi yana murmushi sosai yace "oyoyo the smallest babygirl in this house princess Aneesah" dariya tayi ta kankameshi sosai cikeda murna dan sunason Dad sosai tace "Dad baka fadamana zaka dawoba bamu maka girki ba" dariya yayi yana kallon Asad dakecin abinci kaman ma baisan mutum yashigo falonba yace "it was a suprise Aneesah, Ya akayi bakije school ba" fitowa daga jikinshi tayi tana kara kallon fuskanshi tace "because of my birthday ranan Friday Dad I wanna celebrate" dariya yayi yashafa fuskanta yace "oh my God don't tell me my princess is gonna be 22yrs on friday " cikeda murna tace " yes that I will be 22 of Friday" gyadakai yayi cikeda gamsuwa yace "we will throw a grand party call the event planner na damka mata komi" wani kalan ihu Aneesa tayi tana tsalle tsalle tace "u are the best best of the best Dad bari naje nagayama Ammi kadawo daga UK" tawuce stairs dagudu juyawa Dad yayi yakalli gateman dake rikeda jakanshi yace "zaka iya barin jakan anan katafi" juyawa yayi yafita hakan yasa Dad ahankali yatako zuwa dinning inda Asad ke breakfast abinshi kaman baisan da mutane afalon ba yakaraso ya tsaya akanshi ya tsaya akanshi yana kallon yaron nashi dayake bala'in so, sobana wasa ba yace "are u not happy to see me, kaganni ko sannu da zuwa babu Asad" batare daya kalleshi cikin muryan wulakanci Tashi yayi ahankali sanan yawuce yafita binsu da kallo Hajiya tayi cikeda murmushi sanan ta tashi dinning taje dakanta batare data kirasu Razika ba tazuba tuwo da miyan kuka da man shanu da nama a plate tawuce sama, bude kofanta tayi ahankali tashiga daidai tana karasa saka riga dan fitowanta daga wanka kenan, akan carpet dinta nakasa Grandma ta zaune tray sanan ta zauna tanuna mata gefenta tace "come and sit" karasowa tayi ahankali tazauna, abincin tanuna mata tace "what stain ur cloth Du'a" Murya chan kasa tace "MP ne bansamu na chanza pad ba" gyadamata kai tayi tace "maisa baki nemi Sharif kin karbi wayanki kin sanardani Asad yakoreki ba" hannu takai jin hawaye yazo mata murya chan kasa tace "kawai dayace I should get out yakoreni abin saiya dawomin da memory gidanmu yanda ake korana sama duk inda naje shine kawai nafita dagudu ina kuk......." saikuma tasake sakin kukan shiru Grandma tayi tana kallon Du'a dan from what she's seeing now Allah ne yaciro yarinyar nan yakawota nan danda depression yakashe Du'a tanada real bad memory of gidansu not good ones, idan ance mata yarda tahaifa Zainab zata iyama yarta haka kokuma zata iya tsayawa tanagani ama yarta haka bazata taba yardaba saisa haryau fada take da Mami, haushinta takeji sabida abinda sukama Du'a, matsarda tray abincin Hajiya tayi ta matsa jawota tayi tasata ajikinta tana bubbuga bayanta sosai tai kukanta takoshi murya chan kasa na lallashi tace "I will say and say this again to you Du'a keda komawa gidan ubanki wlh sai inda karfina yakare kinbar gidan nan har abada, kin barshi kenan so stop crying and leave you life, gobe zamuje mufara yin national Id card akwai wanda nasani zai miki yana fitowa sai mubude bank ko duka duka next week kin fara aiki kinji" gyadamata kai tayi, Grandma tace "good girl, Allah yamiki Albarka kinji" ahankali tace "Ameen" Grandma tace "ina kikaje hope nothing happened to you" girgixa mata kai tayi tace "bansan sunan wajenba mai taxi yakaini babu abinda yasameni yunwa kawai yasa nadinga bacci" dan dariya Grandma tayi tace "Alhamdulillah zokici abinci to maza" da kanta Grandma tasa hannu yashiga feeding yarinyar hakan yasa kuma taci abincin sosai kaman ba Du'a ba, tana gamawa paracetamol tadauko tabata tasha sanan tasa taje tawanke hannu tazo kanta tadaura kan cinyarta tana bata shawarwari kan yanda zatai handling any situation datake ciki ko data shiga ahaka bacci yay awon gabada ita. Washegari!! Hakanan yajima baijin zuwa office yau, kasa fitowa yayi dan jiya jiri jiri kin bin Ammi side dinta yayi, ga Sharif yashareshi tun jiyan nan da abin saiyazo yafara damunshi dan yanason dan uwan shi yasaba every minute Sharif ke tsokananshi yasashi surutu. Wuraren 11 yafito daga side dinsu shima yunwa takadoshi, bude kofan flat dinsu yayi yashiga babu kowa a falon hakan yasa yaji bala'in dadi, dinning yawuce kujera yaja yazauna sanan yazuba shayi a cup yasa dan chips da egg a plate yanaci, bude kofan kitchen akayi dayasa dasauri yadago kanshi Aneesa ce tana sanye da rigan bacci daya tsayamata a guiwa mai hannun shimi baki, kanta babu dan kwali, wani irin murmushi tayi tace "laaaa Ya Asad bakaje office ba" dauke kanshi yayi daga kallon kofar kitchen din danya dauka Ammi ce batare daya bata amsa ba, dan turo baki tayi aranta tace "shegen wulakanci ne dashi" adan shagwabe tace "Ya Asad good morning" batare daya kalleta ba yace"morning" yacigaba da in abincin shi, kitchen takoma tajuye Indomie datake dafawa a bowl da egg tadau fork tafito tazo dinning din, kujeran dake facing nashi directly taja tazauna tafaraci, dago kanshi yayi kaman wanda yatuna abu yakalleta yace "why didn't u go to school yau Tuesday"? Dagokai tayi ta kalleshi faduwa gabanta yashiga yi yanda yazuba mata idanu yasa takasa karya ahankali tace "zanje birthday shopping ne birthday dina is this Friday, kuma Mum zatazo on Thursday" baki yabude zaiyi magana aka bude kofan falo aka shigo wani irin ihu Aneesa tayi ta tashi dagudu tai kofan "Daddy oyoyo, Dady oyoyo" tawani irin fada jikin Dad daya shigo yaci bugaggiyar malum malum milk ga gateman biyeda shi rikeda katon akwatin shi, budenata hannu yayi yana murmushi yace "oyoyo the smallest babygirl in this house princess Aneesah" dariya tayi ta kankameshi sosai cikeda murna dan sunason Dad sosai tace "Dad baka fadamana zaka dawoba bamu maka girki ba" dariya yayi yana kallon Asad dakecin abinci kaman ma baisan mutum yashigo falonba yace "it was a suprise Aneesah, Ya akayi bakije school ba" fitowa daga jikinshi tayi tace "because of my birthday ranan Friday Dad I wanna celebrate" dariya yayi yashafa fuskanta yace "oh my God don't tell me my princess is gonna be 22yrs on friday " cikeda murna tace " yes that I will be 22 of Friday" gyadakai yayi cikeda gamsuwa yace "we will throw a grand party call event planner na damka mata komi" wani kalan ihu Aneesa tayi tana tsalle tsalle tace "u are the best best of the best Dad bari naje nagayama Ammi kadawo daga UK" tawuce stairs dagudu juyawa Dad yayi yakalli gateman dake rikeda jakanshi yace "zaka iya barin jakan anan" juyawa yayi yafita hakan yasa Dad ahankali yatako zuwa dinning inda Asad ke breakfast abinshi ya tsaya akanshi yana kallon yaron nashi dayake bala'in so yace "are u not happy to see me, kaganni ko sannu da zuwa Asad" batare daya kalleshi ba cikin muryan wulakanci yace "welcome Dad" tsayawa yayi yay shiru yana kallonshi yanda yake breakfast din ahankali bayako kallon inda yake yay wani irin kyau yakara cika bakinshi na glowing kaman ba Asad din dayake goyawa abayanshi suje park bane yana siyamai all kind of toys, murya chan kasa cikeda damuwa sosai yace "why do you hate me so much Asad?" batare daya kalleshi ba yakai mug din shayi baki zai kurba yace "halinka" sanan ya kurba ya ijiye yadau fork yacigaba dacin Irish da egg dayake diban kadan kadan kaman wani dan baby, shiru Dad yayi yana kallonshi saikuma yay murmushi irin murmushin nan na manya yace "Asad kenan! My one and only Son, forget kawai, forget u are 33 u are still a small boy dabakasan komi gameda rayuwaba, all you focus on is neman kudi sabida ni, u don't want my money, u don't even spend my money Asad ina mahaifinka, sabida ni kaki bama any mace chance tasoka ko kasota, bamaka tunanin aure balle settling down but listen here" Dad yay maganan yanajan kujera dake right next to Asad yazauna very very close to Asad din yana kallonshi yace "kaine d'a daya tall dana haifa aduniyan nan, daga kanka Allah bai kara bani haihuwaba saisa kaga natara gidan nan da yaran yan uwana dan inason yara ni, jinin jikina dakake gani Asad shine ke gudana ajikinki, duk randa zaka kebe da mace Asad u will understand that I am biologically ur father and my blood runs through u, instead of wanan bakin tasnan dakamin kullum kana dana sanin samuna amatsayin uba u could have easily make me ur ally ur best friend and ur partner, I will spoil u da kudi, luxury and different mukami and position in the global market and the Nigerian economy, zan sangartaka nabataka dakomi kaci karenka ba babbaka, babu mai cemaka why kayi kaza or mesa kayi kaza, mata idan duk sakan sakan kakeson sabuwa zaka samu u are rich and ur father is rich kasan irin matan dayake suyi chilling da big boy irinka, mata ma yanzu ingaya maka begging suke acisu ko bazaka basu ko sisi ba kawai u just dull yourself here, office to office abinda ka iya kenan , u don't club u don't do women, u don't have fun da samari masu shekarunka ke having all in the name of u don't wanna be like me, ko shisha nan nan bakasha Asad, yaro har yaro mai jini ajika, two good degree holder amman bakasan komiba na more rayuwa, ni dinan ubanka daka tsana u will come to me one day kace nai cleaning mess din dakayi kuma........." wani irin tura plate din dayake cin abinci dashi Asad yayi yay wani irin kara hakan yasa Dad yay shiru, tashi yayi dagakan kujeran yadau tissue yashare bakinshi yajefar kan table din sanan yakalli Baban nashi disgustingly cikeda tsana yace "I've lost my apatite". 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 3️⃣5️⃣ Wuraren 5 Rahima da Mariya suka shigo gidan daga school ganin Dad a kitchen yana girki yasa duk suka rungume shi cikeda murna oyoyo Dad, murmushi yamusu yadau glass cup ya tsiyaya musu juice din daya hada yace "take this now, dinner is at 7 kuje dakinku kuhuta, Aneesa na gidan Hajiya wai taje wajen kawarta, today am cooking everyone's favorite dish in this house, tun 1 nake kitchen kunga Ammin ku ma her majesty nace tazauna and just be watching me ita kebani energy" yanuna musu Ammi dake zaune tanama yaran murmushi, cikeda murna sukace "Dad u are the best" wani irin fari yamusu da idanu yace "I know that girls kuje kuhuta" duk juyawa sukayi sukai dakinsu, shima Sharif daya shigo gidan around 6 bala'in mamaki yayi ganin Dad shi kadai yanata setting dinning, rungumeshi Dad yayi yacemai yaje yay wanka sutafi mosque yagama komi, sosai yake mamaki kannema Ammi idanu yayi irin iyye dinan sanan yawuce yatafi side dinsu, ganin Asad zaune afalo yana aiki a system yasa yadaure fuska yawuce, dan murmushi Asad yayi yace "are you gonna be staying angry for forever"? juyowa Sharif yayi yakallehshi batare dayacemai komiba, kannemai idanu Asad yayi yace "yes I want to know sabida insan kozanje na nemo wani brother ne ko saya akeyi in siya atoh" kwafa Sharif yayi yajuya yahau stairs yace "try it kagani wlh" dan dariya Asad yayi yace "I love u too" sake juyowa yayi yadaure fuska yace "who said I love you" dan sosakai Asad yayi yace "I thought u just said that" hararanshi shima Sharif yayi yacigaba da tafiya abinshi saida yakai gaban dakinshi sanan ya tsaya daga murya yayi yace "apology accepted, lemme shower nasauko muje mosque" daki yashiga wanka yayi yafito yasa wasu simple kaya sanan yafito Asad yagani dahar yay alwala yasaka wani simple riga da wando na yadi milk yasha guga, fita sukayi daidai Dad na fitowa shima daure da alwala yace "wait for me boys" tare suka jera zuwa masallaci Sharif ne kawai ke amsa hiranshi Asad ko uppan baice mishi ba, ana sallanewa baima tsaya zikiri ba yafito dan baiso sujero tareda Dad. Shigowa sukayi gidan shida Sharif suna hira, falonsu suka shiga yahau kwalama kowa kira. "Wife, Children time for dinner a sauko" yay maganan yana zuwa sama, dakinshi yashiga baijima ba yafito yasauko kasa, dukansu suna zaune a dinning harda Ammi Asad ne kadai baya wajen, dan jim yayi saikuma yakaraso yazauna yana musu murmushi yakalli Ammi yace "jekira Asad Sweetheart, today is a special night, I've come back nama kowa girki yau, call him" gyadamaikai tayi ta tashi daga wajen, Rahima dake murna sosai tace "Dad nabude warmer meka dafa" tamika hannunta zata bude dasauri yace "bar bar bari, it's a suprise bari Asad yazo kowa zai bude abincin shi" duk murmushi yaran suke, Mariya tace "Dad I've missed ur food sosai wlh kai chef ne" Aneesah tace "ni wani zubin kasa gane abincin wa yafi dadi tsakanin shi da Ammi" dariya kowa yayi daidai lokacin Ammi tabude kofan falo tashigo Asad biyeda ita yana tafiya ahankali fuskan nan nashi babu alamun wasa, ahankali Dad yasauke ijiyan zuciya ganin yazo sanan yatashi dasauri yajama Ammi chair yace "come sit Sweetheart yau ko tsinke bazaki dagaba kaman yanda nai promising" dan murmushi Ammi tayi tana mamakinshi zama tayi ahankali ya tsaya tabayanta yadaura hannayenshi kan kafadarta yanadan satan kallon Asad dayaja kujera kusada Sharif yazauna yana kokarin ciro wayanshi, murmushi Dad yayi yace "tom bari mufara zan bude abincin kowada kaina I will start dana love of my life, my wife that always support me and help me keep this family together" murmushi duka yaran suke banda Asad dako kallonsu baiyiba, hannu yasa yabude warmer dake gabanta lafiyayyen tuwon shinkafa ne da miyan taushi da nama, murmushi Ammi takakalo tace "wowwww, ohh banmasan mezance ba, thank u hubs" cikeda siyasa yace "don't thank me peck me anan I prefer that" yay maganan yana nuna mata kunatun shi dan yadauko ta saitin kunnenta, ahankali tai pecking nashi, yaran sukahau ihu barinma Aneesa, komawa gefe yayi yazauna yana gyara zama yace "children u can all open Warners din dake gabanku" kaman jira suke dasauri suka shiga bude bude kowa was in awe dan Dad ya dafa fav nashi, ganin Asad ne kadai ke budeba yasa yace "saura kai Son, open it" yay maganan yanamai murmushi dasauri duka yaran suka kalleshi, Sharif dake gefenshi yace "bude muga mai Dad ya dafa maka kagani yamin fatan doya banmasan ya akayi yasan is my fav ba" dan dariya Dad yayi yace " I know everything, open Asad" ta kafa Sharif yataba Asad akarkashin table din hakan yasa ahankali ya ijiye wayanshi yakai hannu yabude warmer rice da bean da mai da yaji da yankaken veggies wowwwwohohoo duka yaran suka shiga ihu dan kowa yasan Asad da shinkafa da wake, murmushi sosai Dad yakeyi yace "you see all na gayamuku babanku is the best" dasauri yaran sukace sure u are dad. Gyaran murya yayi hakan yasa kowa na table din yayi shiru yace "kafin mufara cin abincin there's something I need to do agabanku" duk tsayawa sukayi suna kallonshi tashi yayi ahankali sanan yaja kujeran dayake kai baya, ahankali yay kneeling agaban Ammi da duka gwiwowinshi biyu akasa, ware ido yaran sukayi cikeda mamaki, hannunshi ahankali yamika ya karbi hannun Ammi dake kallonshi cikeda mamaki dan this part he's playing batasan na menene ba, chanza fuskanshi yayi zuwa serious regret face yana kallon Ammi, ahankali yace "Children bazan muku karyaba nasan Ammin ku hid everything from u all but nama Ammin ku laifi sosai da idan natuna abinda namata inaji na tsani kaina" yay dan shiru yana sauke ijiyan zuciya ta gefen ido yake satan kallon Asad dayaga har lokacin kanshi nakan wayan dayake dannawa hakan yasa yasake gyara murya yace "kunga Zainab is the best wife da kullum ina addu'a Allah yabama Asad da Sharif mata tagari kaman Ammin ku, tamin komi she has been patient and understanding dani she never complains, tanamin kome nakeso but dudda haka I hurt her" yasakeyin shiru yace "namata babban laifi da I can't even tell u people abinda namata but all I know is I regret everybit of abubuwan dana mata, how can I hurt this beautiful woman mai beautiful heart datake rainanmin yarana tana basu best tarbiya how can I" yay maganan muryanshi na narkewa dayasa kowa yay tsit har Asad dake danna waya daina dannawa yayi but still bai kallesu ba, ganin haka yasa yace "matar nan tamin komi, and I am a bad person Nagano kuskurena and I am very very sorry, saisa I am using this chance nabata hakuri naroketa tayafemin agabanku and I want to promise her bazan karaba nabar halin nan har abada and I will be that husband datake so nazama, I will stay by her side and support ba bazan karaba, bazan karaba Zainab, kinyafemin?" yay maganan ahankali yana kallonta dayasa takasa koda motsi kallonshi kawai take dan batasan ko this part is real or fake ba, Ahankali Asad yadago kanshi yakallesu, dukta gefen ido yake kallonshi, wani irin narke fuska yayi yace "I am truly very sorry I will never hurt u again, kinyafemin?" Jin Ammi still tai shiru yaranma sunyi tsit yasa yajuyo yakalli yaran da idanunshi dasukai ja kaman wanda ke shirin yin kuka yace "kutayani rikon Ammin ku please tayafemin nasan namata laifi but I am on my kness begging" yay maganan ahankali yasake juyawa yadaura kanshi akan cinyanta yay shiru, kallon Ammi Sharif yayi ahankali yace "Ammi forgive Abba let's move on and forget the past right Asad" shiru Asad yayi baice komiba, Rahima tace "Ammi please" su Rahima ma suka shiga cemata please dan murmushi Ammi ta kakalo takai hannunta tadaura asaman kanshi ahankali tace "nayafemaka Baban Asad, Allah ya yafemana gabaki daya" wani irin rungumeta yayi yaran sukahau ihu harda Sharif, Dad yace "thank you Thank u so much wife, Allah yabarmu tare mu aurar da yaranmu, wait I have a gift for u" yay maganan yana tashi tsaye da sauri kitchen yashiga saigashi yafito dawani jan box da akai wrapping, bata yayi yace "open it" karba tayi tasauke kan table dasauri Rahima tace "wlh I must video this, Dad is the best Allah ya iya soyayya, Allah yabani miji kaman Dad nima nai sona" kallonta Asad yayi saikuma yacire kai yamaida kanshi kan Ammi yaran kuma suka fara video, cire wrapping shit do tayi saiga wani jan box ahankali tabude wani lafiyayyen sarkan zinare ne da tsayinshi zaikai cikinta da dankunne da warwaro da zone da akalla worth dinshi zaikai 55M, wani irin ihuuu su Rahima sukahau yi suna buga dinning table din, Ammi kasa rufe baki tayi ganin saka har sarka, matsowa Dad yayi yace "bari nasamiki" daukan sarkan yayi ahankali sanan yadawo ta bayanta duk yaran na video sanan yasamata awuya ahankali sarkan har kan cikinta tsawonta gashi yama Ammi bala'in kyau ihu yaran sukahau yi, dan murmushi kadan Asad yayi yadau fork yasa a warmer yace "Zinariya left shine yanzu kagane worth din Ammi na". Sosai Dad ke satan kallonshi ganin yana murmushi harma yadau fork yanacin abincin dabai taba expecting zaiciba yasa yay murmushi aranshi yace "yaro man kaza, badai ur mother is ur weak point ba, I will shower her with love agabanka just to win u back, watch and see how I will brush ur life Asad..." 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 3️⃣6️⃣ Murmushi Sosai Dad keyi yakalli su Rahima dake musu video yace "it's okay children now let's all eat and pray Allah should always keep this family happy and united" zaunarda Ammi yayi yazauna agefenta yana feeding nata abincin, saida suka gama tass sanan yashare baki yakalli duka yaran yace "so the smallest lady in this house birthday is on Friday, zamuyi celebrating, what time kikace kinaso ayi celebrating din"? yay maganan yana kallon Aneesa dake washe baki kaman anbata kyautan kujeran makka tace "Dad da daddare, I wanna make it dinner, all my friends yan Nile will be coming" murmushi yamata yace "it's fine, ur Mum tacemin zata shigo on Thursday jibi kenan, dan haka afara shirye shirye" yakalli Ammi yace "kiyi calculating komene kuke bukata and let me know" dan murmushi tayi tace "birthday ai nata ne itada kawayen ta, babu abinda nake bukata" gyadamata kai yayi cikeda gamsuwa yace " in that case, tashi mutafi sama abinmu muyi hira" yay maganan yana kama hannunta sukai sama yarinyar suka shiga ihu, dasauri Aneesa ta taso tazo kusada Sharif tana satan kallon Asad dake daddanna waya tace "Ya Sharif kaga Du'a itace Babban kawata" dan zaro idanu yayi yana tura baki yace "su Aneesa manya yaushe Du'a tazama best friend dinki kuma" dan murmushi tayi tace "run randa nafara ganinta tanada kyau" bayan Asad yataba yace "tashi kaji mutafi dakinsu I am so tired" tashi Asad yayi yana maida wayan dayake aljihu yawuce yabi bayan Sharif suka fita daga flat din Aneesa nabin Asad da kallo, wani irin dariya Mariya tayi tace "yarinya kinada aiki" dawami irin sauri Aneesa tajuyo takalleta danjuyamata ido tayi tace "dake nayi kike wani kallo na tashi nidai mu gyara dinning muje mu kwanta. Suna fita Sharif ya matso kusada Asad yace "is that really Dad kodai mafarki nakeyi ne Asad" tabe baki Asad yayi yace "ohon mai" dasauri Sharif ya harareshi yace "common kaikuma saikace wani shaidan, look at what happen publicly Dad yabama Ammi hakuri fa, you know Dad ya chanza Alhamdulillah wlh naji dadi sosai, please kaima kayafemai kawai let's all live in peace and harmony" tabe baki Asad yayi batare dayace komiba yabude flat dinsu suka shiga tare. **** Wuraren 9 bayan angama breakfast Dad ya kwashi Rahima da Mariya yace zaiyi dropping nasu a school daganan yawuce office Sharif shima yawuce aiki, daga Asad wanda yamakale adaki sai Aneesa da Ammi ne agidan, shi karan kanshi yarasa meke damunshi he's not just in the mood for office ne maybe gajiyane dan last week he work all through aikin TV. Wuraren 9 event planner da akabama contract din birthday din Aneesa yazo yakawo lodin kayan souvenirs dinta, power bank, water bottle da set na makeup brushes ne da duk aka rubuta happy birthday ajikinsu saikuma hadaddun jakunkunan da zasu saka su aciki, ana kawowa tazura hijabi tafito Ammi dake falo tace "sai ina kuma" cikeda murna tace "Ammi zanje in taho da Du'a ta tayani hada this souvenirs a bags dinsu" haba Ammi takama tace "iyye masu birthday a dawo lpy" dagudu tafita tana murna gidan Hajiya tayi, da sallamanta tashiga falo Hajiya na zaune wani irin gudu tayi tafada jikin Grandma tace "good morning Hajiya Naaa" "jama'a na shiga uku, wlh nakusan hana yaran Ammi shigomin gida hakanan bazaku takaitani ba" dariya tayi ta tashi daga jikinta tace "wlh ko kinsa kwado saimun karya, ina Du'a Hajiya? Ankawo souvenirs dina zamuje gida muyi packaging nasu ajaka ne" tabe baki Grandma tayi tace"jetana sama, ni wlh ku tattara kutafi chan wajen Ammi ma yafimin, wanan hiran birthday naki ya isheni Aneesa" dariya tayi tace "Au haka kikace shikenan aiko bazan bari tadawo na agidanmu zata kwana yau" tai maganan tana hawa stairs, dakin Du'a tabude ahankali, zaune taga Du'a tasanya wani farin Paris t-shirt fari kall ga zanen effiltower tower ajiki, da bakin english skirt mai belt data saka dayawani irin fitoda hips dinta, kanta babu dan kwali amman tai parking kalabanta atsakiyan kai tana zane a drawing book tai bala'in kyau, dayake hankalin ta yay nisa bamataji shigowan Aneesah ba, ahankali Aneesa tamaida kofan tarufe sanan takaraso tasa hannu ta fizge drawing book din dawani irin sauri Du'a tadago kanta, kafin ma tai magana Aneesa takama hannunta taja cikin sauri tace "tashi kigani Du'a" tashi tayi Aneesa tasaketa tashiga waige waige bakin hulanta datagani kan gado tadauko tazo dasauri tashiga samata akai tace "ankawo abubuwan gift muje kitayani muyi paking ajaka" tai maganan tanayin hanyan wardrobe wani karamin dark blue hijabi ta janyo mata tadawo tabata tace "sa muje" kallonta Du'a tayi kaman mai tsoro tace "gidanku" gyadamata kai Aneesa tayi tace "eh" ahankali Du'a tamake mata kafada tace "ni bazani ba kunya nakeji" dasauri Aneesa tace "babu kowa agidan fa dagani sai Ammi daga Ya Sharif har Ya Asad duksun tafi office, su Rahima sun tafi school sunada presentation dukansu, nida Ammi ne kawai kinga kuma babu mai tayani please sa hijabin" tai maganan tana karban hijabin tasaka mata bata jira amsanta ba taja hannunta suka fita daga dakin sukai kasa, a falo suka tarar da Grandma ganinsu yasa ta tabe baki tace "agais nidai bye ku gaidamin da Ammin ku" sosai Aneesa ke jin dadi tace "zataji ai gashinan ma zan kai Du'a gidan mu daman bata taba zuwaba muje kiga gidanmu" Du'a naji tana gani tajata suka fita daga Gate dinsu suka shiga next babban gidan dake kusada su, bin gidan take da kallo gidan Babban gaske dan yamafi na Grandma girma ga tulin motoci ga security daban daban dayawa da abinma saiya bata mamaki saikace gidan yan sanda. Ahankali Aneesa tabude kofan falo tana rikeda hannun Aneesah, ganin su yasa Ammi dake zaune kan kujera tace "Du'a nake gani agidana wato sabida kawarki ce zakizo gidan nan ba sabida kizo ki gaidani ba ko" akunyace tasauke kanta kasa hakanan take bala'in jin kunyan matan murya chan kasa tace "ina kwana Mum" "lpy lau Du'a, how are u" ahankali tace "Alhamdulillah" tashi Ammi tayi tace "come kin tsaya daga wajen ga kayayyakin nakunan ai am cikamin falo dasu" karasowa ciki Du'a tayi ta tsaya, Ammi tace "bari naje sama na kwanta feel at home ko" gyadamata kai Du'a tayi Ammi tai sama abinta, hijabi Aneesa tacire tana linekwa daga ita sai kayan bacci, karasowa kusada Du'a tayi tazare hijabinta tace "bari naje na ijiye mana hijaban adakinmu nazo kigani mufara" wucewa sama tayi hakan yasa Du'a tazauna ahankali akasa tana kokarin jan hulan da Aneesa tasaka mata gaba dan bai rufemata gaban kai da kyau ba ana ganin kitsonta tagaba da kwantaccen gashin goshinta, saukowa Aneesa tayi tazauna kusada ita tace "kinga wayan nan bags din kowanne zamusa 1 water bottle dinan, da powerbank dinan dakuma set na makeup brush dinan, ke gashima baki makeup ai wlh gobe saikinyi, gobema zamuyi aiki da yawa zanje na karbo kayan da zansaka awajen hudayya, kema harda naki zan karbo" bude idanu Du'a tayi tace "nawa kuma" gyadamata kai Aneesa tayi tace " Ya za'ayi birthday na guda nayi dinki banma best friend dina ba" dan murmushi Du'a tayi ita bata tabayin friend ba saisa idan Aneesa nakiranta best friend saita dinga jin abun wani bambaran. Hada kayan suka shigayi suna jera jakunkunan anan falon, tashi Aneesa tayi dasauri tana kama cikinta tana yatsine fuska dasauri Du'a tace "menene" hanyar stairs tayi tace "continue ina zuwa lemme use the bayi, cikina na juyawa I guess I am too excited ne" dan dariya Du'a tayi batace komiba tacigaba da abinda takeyi ahankali aka bude kofan falon dawani irin sauri tadago kanta, hada ido tayi da Asad dake sanye dawani dark blue 3quater da farin t-shirt yana wani irin zuba uban kamshi fuskanshi yadan kumbura alamun baidade da tashi daga bacci ba, wani irin faduwa gabanta yayi dawani irin sauri tadauke kanta tana saukar da kanta kasa, gyara zaman kafanta tayi takai hannunta tanajan skirt dinta yarufe mata kafa duka dan yadan tattaro zuwa wajajen gwuiwanta sabida yanayin zaman datayi da jakan datake ijiyewa in between legs dinta tana saka souvenirs din aciki, wani irin ijiyan zuciya tasauke feeling so uncomfortable sabida yanayin kayan datasaka, ahankali taja jakan daga tsakiyan kafanta tadaura kan cinyanta sabida yadan rufe boobs dinta dasukai girma ta farin t-shirt din sanan kana hango shape da komi na bra jikinta sabida very light expensive t-shirt ne, jin shiru bataji sahun tafiyanta ba yasa tadan dago kanta kaman munafuka tana kalle kalle, a dinning din falon taganshi tsaye yadaga flask yana zuba ruwan zafi a mug yana kokarin hada coffee, batasan mesaba amman kasa daina kallonshi tayi shigan dayayi yamata kyau saiyay kaman wani dan gayu, juyowa yayi dawani irin sauri tadauke kanta kirjinta na dukan uku uku, daukan mug din yayi yazo cikin falon kujeran dake facing nata yazauna akai tareda mika hannu yadauki remote yakunna TV yasaka a tashan ball sanan yayi sanan ya ijiye remote din yay crossing legs dinshi yakai mug din bakinshi yayi sipping coffee ahankali yana kallon TV. Kasa cigaba da abinda takeyi tayi, gabaki daya jitayi she's so uncomfortable, sai gyara nan da nan da nan take na kayan jikinta, daidai nan Aneesah tasauko kasa ganin Ya Asad yasa ta ware idanunta tace "laaaa Ya Asad daman bakaje office ba" ko kallonta baiyiba haka yasa tawuce kusada Du'a zata zauna yace "make me some omelet ki kawomin part dina" dasauri takalleshi cikin wani irin jin dadi jin yakulata tace "tom Ya Asad" sanan tawuce kitchen, tashi shima yayi rikeda mug din yawuce yafita daga falon, wani irin ijiyan zuciya tasauke tacigaba da aikin har lokacin takasa dainajin kamshin dayakeyi. Kusan 10min Aneesa tadauka a kitchen tana hadamai lafiyayyen Omelet sanan tafito rikeda hadadden tray data daura plate din Omelet din akai, daidai lokacin aka bude kofan falo wata hadaddiyan faran mata tashigo tana sanyeda Abaya tanama Aneesa murmushi, wani irin tsalle da ihu Aneesa keso tayi tunawa da abincin waye ke hannunta yasa ta ijiye kan hannun kujera dasauri sanan tawani kwasa da gudu tafada jikin matan saikuma kuka. "Oyoyooo Mum, bakincemin gobe zakizo ba" kankameta matan tayi tace "I wanted to suprise my birthday girl" tai maganan tana kallon Du'a dake kallonsu tana murmushi dan taga kamanninsu da matan hakan yasa tagane itace Maman Aneesa, sakin Maman nata tayi tajuyo takalli Du'a tace "Mum kinga best friend dina sunanta Du'a" wani irin kallo Turai tabi Du'a dashi, ahankali Du'a tace "ina yini" lafiya ta amsa sanan takama hannun Aneesa tace "muje sama" juyowa Aneesa tayi takalli Du'a tace "Du'a please tayani kaima Ya Asad Omelet dinshi yanzu karyamin fata, kina fita flat dinsu ne a gefen namu kinji please, baiyi breakfast ba" gyadamata kai Du'a tayi ahankali tana kallon yanda sukebinstairs Mum dinta namata magana, harsunkai karshen stairs Aneesa takara juyowa tace "Du'a hurry karya huce bazaici ba" tashi tayi jikinta har bar bar yake tadauki tray data ijiye kan kujera sanan tawuce tafita hakan yasa Aneesa sukai ciki, flat din datagani kusada nasu tayi, ahankali ta tsaya gaban kofan tama rasa mezatayi she's so nervous hakanan, door bell datagani ta danna ahankali, daga taciki taji ance come in. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 3️⃣7️⃣ Takai kusan 1min tsaye takasa tura kofan tashiga dakin kuma ba'a kara cewa komiba daga ciki ba, kaman ta ijiye abincin anan gaban dakin takeji amman kuma bai daceba dan Aneesa bamata rufe plate na Omelet dinba, daurewa tayi ta mugun daure sanan ta tura kofan ahankali tasakanta ciki, wani irin sanyi da kamshi ne yamata sallama danya Kure AC dakin yana zaune kan kujera ga mug din coffee dinshi agefe saikuma MacBook kan jikinshi yana danne danne, ganin ko dago kanshi baiyiba balle ya kalli kofan yasa tashigo cikin dakin gabaki daya tamaida kofan tarufe takaraso ciki kafanta na harhardewa kaman zata fadi gawani kalan kunya datakeji sabida yanda babu dogon riga ko hijab ajikinta, dan karamin table din dake gabanshi da mug din tea kekai ta kalla dan dagakai tayi takalleshi batare data kara so wajen ba, lips dinta tadan lasa jin yawani irin bushe kafin ahankali cikin yar muryan nan nata tace "unnnn, Aneesa tace nakawo maka unnn....wanan" tadaga tray tana nunamai kaman yana kallonta, dan table din gabanshi yanuna mata batare daya kalleta ba yana aiki akan system dinshi, dan ajiyan zuciya tasauke sanan tashiga takawo ahankali takaraso gabanshi ahankali tadaura tray akan table din ta tashi dasauri zata wuce batare daya kalleta ba kawai yasamata kafa jikake tipppp tai wani irin mugun faduwa danma Allah yataimaketa akan rug ne inda a tiles ne da halan saita karye amman dudda haka ta bugu barinma kirjinta dan akife tafadi, wani irin malalacin kara tasaki na wahala. "wayyooo Allah na Mamiii na mutu" sai kuka ahankali tasakeshi tana kokarin tashi, ahankali yadauke system dinshi daga kan jikinshi ya ijiye agefe sanan yajuyo da kanshi ya kalleta daidai ta tashi zaune da kyar tana goge hawayen kan fuskanta hulan kanta shima yacire yay chan gaba, hada ido sukayi wani mugun kallo yamata yace "that's for not greeting me, duk randa kika kara ganina kina bina da wayanan idanun naki batare dakin gashiniba saina miki wanda yafi wanan" gyadamai kai tayi ahankali tana goge hawayen dasuka kasa daina zubomata, da kyar saida ta dafa kujera sanan ta iya samu ta mike tsaye hakan yasa kalban kanta suka wani zubo har waist dinta, hawaye tasake sharewa sanan ta tsugunna tadauki hulanta sakawa tayi tagoge fuskanta tass sanan tawuce tai kofa harta bude kaman daga sama taji yace "feel free kigayama Ammi ko Hajiya, zakiga abinda zan miki stupid girl" dasauri tafita daga dakin tamaida kofan tarufe, anan bakin kofansu ta tsugunna saida tasha kuka sanan ta share fuskanta tass tarasa maisa ya tsaneta haka, all she ever did was trying to tell him thank you kan abinda yamata, saida tagama tass sanan ta tashi ahankali tasauko tana tafiya akasa, hango pampon wajen flowers din gidan datayi yasa taje wajen, ahankali ta tsugunna tabude pampon ta tara ruwa ahannunta tana wanke fuskanta sanan tazare hulanta tasa akan kafanta ta tattare gashinta ta tufke dan batason sakin gashi sanan tamaida hulan tamike tsaye tajuyo, hada ido sukayi dashi yafito yana tsaye gaban dakinsu rikeda waya a kunne yanayi dawani irin sauri tadauke kanta kaman tada dodo sanan tawuce main flat. Bude kofa tayi ahankali da sallama tashiga Aneesa tagani tana saukowa tace "yauwa Du'a thank u, kinsan Mum dina akwai masifa, tafi kowa masifa aduka family mu saisa kowa tsoronta yake dan bata wasada yara, inda ban bita ciki ba dana shiga uku da masifanta" tai maganan tana karasowa gaban Du'a ganin idanunta yasa tace "maiya sameki kuka kikayi?" girgizama takai tayida sauri tace "a'a wanke fuska nayi a tap din danagani awajen flowers idanuna sunyi jane" hannunta Aneesa takama tace "eh sunyi ja maybe kinsa ruwa acikin idanun ne zomuje mucigaba da aiki" zama duk sukayi suka cigaba da aikin dasukeyi saikuma chan tadago kanta tace "akwai abinda ke damuna Du'a bantaba gayama kowaba harsu Rahima, dudda nasan bakida any saurayi but I want to tell you sabida nauyin abin azuciyata yaragu the burden is too much for me" yanda tai maganan kadai yasa Du'a ta lura dakoma menene abin na mugun damunta, hakan yasa takama hannunta tarike kaman yanda taga Grandma namata idan tana kuka tace "menene Aneesah" kallon Du'a din tayi for some secs sanan murya chan kasa kaman mai whispering tace "is Ya Asad, wanan dayasani nasoyamai kwai dinan, Mai kamfanin dakike ma zane" gyadamata kai Du'a tayi tace "yacika mugunta ko" dariya sosai Aneesa tayi tace "mugunta ai tambarin Ya Asad ne kowa yasani but wlh yamafi Ya Sharif kirki Allah kuwan" gyadamata kai kawai Du'a tayi batare datace komiba, ajiyan zuciya Aneesa tasauke tace "Du'a wlh ina bala'in sonshi, mahaukacin so nakemai sosai, kinga cousin dina ne, Mum dina dinan dakika gani tazo kanwar Baban shine, ni bantabason wani namiji kaman yanda nakeson shi ba amman kallo ma ban isheshi ba wlh, bansan Yaya zanyi ba, I don't know, ai kinga irin giran damuke yi a group nasha nasa kayan bacci nasa shimi harda towel ma naje wajenshi tambayan wani abu amman ko kallo ban isheshi ba baima nuna yana ganina ba balle inma sa rai, nakasa kula kowa, shikuma baimasan ina existing ba, Yaya zanyi eh Du'a, please ki gayamin mezanyi" dan zaro ido Du'a tayi tana kallonta ita bama tasan mezata mataba, duka yan kalaman bakinta dasuka rage tatattaro tace "kigaya mishi to" zaro idanu Aneesa tayi tace "ke Du'a sokike ya kasheni, wlh ko kare ya cijen bazan iyaba, ko zaki tayani fadamai" dawani irin gudu Du'a tasaki hannunta takoma baya, dariya Aneesah tayi tace "ke dalla chan I was just joking nasan bazaki iyaba but I will need ur help, inama wayanki" tajuya dasauri tana neman wayan Du'a, daukan wayan tayi dagakan saman kujera tabude dayake ba key tana danne danne, matsowa kusada ita Du'a tayi tace "me kikeyi dawanaya" bata amsa Du'a ba saida tagama danne dannenta sanan tadago kanta tana murmushi tace "done" dasauri Du'a tace "me kikayi" wani irin murmushi tayi tace "text naturamai" faduwa gabanta yashigayi tace "text kuma Aneesah dawayana" "eh aini yanada number na kekuma baidashi, yanzu dai kowani kalan reply kikagani kituromin banson kiga text din danamai dannai deleting kina ganin reply kituromin" kaman zatai kuka Du'a tace "kinga karki sani a matsala wlh ni tsoron shi nakeji" dariya Aneesa tayi tace "dalla babu abinda zai miki keda bamakisan maina turamai ba, now let's continue munkusan gamawa ma" cigaba da hada kayan sukayi saida suka gama tatas sanan suka shiga jera kayan a store na kasa, suna gamawa tace "zantafi kawomin hijabina" Ammi dake saukowa ne daga sama tace "ai baki isaba keda komawa sai dare" akunyace ta sunnar da kanta, Ammi takaraso tace "oya kuzo kutayani aiki a kitchen" dariya Aneesa tayi tace "yauwa Ammi daman banso ta tafi" Ammi tace nima haka, sosai Ammi tashiga ko yamusu girki barinma Du'a datafi maida attention akanta, itadai Turai ko fuska batasakin ma Du'a din ballame tamata magana, da kyar Du'a tasamu da magrib Ammi ta barta ta tafi danda su Rahima duk hada baki sukayi sukace saita kwana dan gobe tun safe zasu fara prep, tafiya tayi bayan tamusu alkawari da sassafe zatazo. 💫KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 3️⃣8️⃣ Ko breakfast din kirki Aneesah batayiba ta tashi daga dinning, Dad yace "ina zaki" murmushi tayi tace "zanje nakira Du'a ne Dad mufara prep we have alot of work ko Ya Rahima" gyadamata kai Rahima tayi, Turai dake zaune itama tana breakfast tace "nifa banson tarin kawayen nan naki Aneesa and u know that" dasauri Sharif dayake shirye yaariga yasa kayan zuwa office ash color suit yace "Mum jikan Hajiya ce fa yarinyar batada matsala ga hankali" kallon Turai Ammi tayi da murmushi kan fuskanta tace "karkiji wani abu Anty Turai all friends dinsu nasansu so ba matsala" yatsine fuska tayi tace "shikenan" dasauri tace "intafi" kallonta Dad yayi yace "tunda Ammin ku ta aminta da ita yes go and call ur friend" wani irin tsalle tayi tawuce tafita, juyoda fuska Turai tayi takalli Ammi tace "yanzu sabida danki baida tarbiya tun jiya nazo gidan nan amman baisan dayazo yagaidani ba, kowa yazo yagaisheni banda shi" kafin Ammi tai magana Dad yace "kinga karki takurama Asad yaron nan is very busy u know that, probably aiki yake saisa baki ganshi but I am sure zaizo yaduba ki ni kaina tun jiya banganshi ba" kwafa tayi bata kara cewa komiba, tashi Sharif yayi yana goge bakinshi da tissue yace "natafi" murmushi Ammi tamai tace "adawo lpy Allah yabada sa'a Son" Ameen yace yawuce yafita yay hanyar kofa, bude kofa yayi yafita yana tafiya zuwa wajen parking space aka bude gate din, Aneesah ce tashigo tareda Du'a dake sanye dawani black dogon hijabi mai hula da kan hijabin yadan mata yawa hakan ya bayyana gashinta dayake looking so black and silky, ganinsu yasa ya tsaya a wajen tareda folding hannunshi a kirji yana kallon Du'a, dan murmushi tayi ganinshi tadauke kai zata wuce yace "wlh kizo nan inba hakaba nida ke ne" juyowa tayi takalleshi saikuma ta makemai kafada alamun bazata zoba, dawani irin sauri yazo wajen gabanta yasha tareda kama waist dinshi yakalli Aneesa dake kallonshi tana murmushi yadaure fuska yace "Ke wuce daganan" makemai kafada tayi tace "Ya Sharif bafa wajenka tazo ba wajena tazo" hararanta yayi yajuya yakalli Du'a, ahankali tace "good morning" murya chan kasa yace "yaushe zaki dawo office" dan kallonshi tayi saikuma ta turo baki tace "Grandma tace ranan Monday" yana kallonta still ko kyafta idanu bayayi yace "kin bude bank din" gyadamai kai tayi tace "jiya Grandma ta kaini wani wuri akamin national I'd card aka bani awurin shine mukaje bank tasa aka budemin account" dan ajiyan zuciya yasauke yace "good" da juyawa yayi ganin still Aneesah na wajen tana kallonsu yasa yace "lemme go to the office don't let this girl stress u kinji" gyadamai kai tayi ahankali batare data kalleshi ba dan batason kallon dayake mata this days, ahankali yana kallonta still yace "bazaki min bye ba" kallonshi tayi saikuma tadaga hannunta tamai waving alamun bye, juyawa yayi yawuce wajen mota sanan itama tacigaba da tafiya tareda Aneesah, hada ido tayida Asad daya fito daga flat dinshi sanye da singlet da 3quater yanadan lankwasa wuya alamun yagaji, dasauri Aneesa tace "good morning Ya Asad" gyadamata kai yayi yana saukowa daga staircase din gaban dakinsu, ahankali tabude kofan falonsu dasauri Turai ne kawai zaune afalon dan kowa yatafi sama shiryawa, murya chan kasa Du'a tace "ina kwana" batare data kalleta ba tace "lpy" murmushi Aneesah tayi takama hannun Du'a tace "muje dakinmu" taja hannunta ganin yanda fuskanta ba Rahama dakinsu tabude mata suka shiga su Rahima na arranging kayayyakin dazai amfani dasu anjima. Saukowa Dad yayi kasa yana sanyeda manyan kaya Ammi biyeda shi, kanwar tashi yakalla yace "bari naje office Turai, yau inada meeting daban daban saikun ganni" murmushi tamai tace "a dawo lpy" juyawa yayi yakalli Ammi dake biyedashi murmushi yamata yace "bye sweetheart" ahankali tace "Allah yabada sa'a" gyadamata kai yayi yawuce yafita daga falon, instead of yay wajen motanshi wani gini dayake gefe daban agidan ginin nada fadi sosai, bude kofan yayi ahankali yanajin karan sauti dake tashi, babban gym ne sosai wajen ga all kinds of machines awajen, Asad dake gudu a treadmill ne yana zufa sosai yajuyo jin anbude fuska, ganin Babanshi ne yasa yadauke kai yacigaba da abinda yake, ahankali Dad yamaida kofan yarufe sanan yashigo ciki home theater dake bada duma ya kashe dakin yay tait sai karan machine din da Asad ke gudu a kaine kadai yarage, karasowa yayi yatsaya gefen Asad din yana kallonshi ahankali yace "Morning Son" dan kallonshi Asad yayi yadauke kai ahankali yace "good morning Dad" cikin wani kalan yanayi na damuwa Dad yace "Asad wai ya kakeso nayi da raina ne eh? Nayi nadaman komi, I've asked Ammin ka for forgiveness ko ita ta yafemin, ina gida bana fita inba fitan office ba but still kana ignoring dina bamaka shigowa side dinmu, haba Asad eh, me kakeso" hannunshi yasa ya kashe machine din sanan yakalli mahaifin nashi yace "I was busy working indoors saisa banshigo side dinku ba bawai sabida kai ba" wani irin murmushi Dad yayi cikedajin dadin respond dinshi yace "to maisa bakazo ka gaida Turai ba" yatsine fuska yayi yace "Dad I don't like her tacika fada da surutu" yay maganan yana wani batarai, dan dariya Dad yayi saikuma yanamamakin sarauta da iskanci iri na danshi cikeda lallashi yace "kowa yasan Turai sai ahankali, but baidace ba yanda bakaje ka gaidata ba tun jiya kana gidan nan kuma, kagama kai wanka saika shiga ka gaidata kaji" yatsine fuska yayi, zai kunna machine din yacigaba Dad yace "wait" kallon Dad din yayi da sauri, dasauri Dad dake kallonshi yace "duko kaga kasan kafini tsowo akwai abu akanka ne zancire maka" ahankali yadan duko batare dayay tunanin komiba, peck Dad yasakinmai agoshi ahankali yace "I love u alot Asad, bari naje" yajuya binshi da kallo Asad yayi saikuma yay dan murmushi yakunna machine din yacigaba da exercise dinshi. Wuraren Eleven suka gama arranging duka kayan, Rahima takalli Du'a tace "Du'a tashi kifara wanka mu bari mukai kayan kasa sai muje wasu dakuna muyi wanka sabida muje shagon hudayya mu amso kayanmu" gyadamusu kai tayi tace "kayana na gida" hararanta Mariya tayi duk suka tsaya suna kallonta Aneesah tace "mu bamuda kayane halan jekiyi wankan karmuyi latti" gyadamusu kai tayi sukuma suka kwashi kayan suka fice itakuma tawuce tashiga bayinsu. Sauka kasa sukayi suna ijiye kayayyakin a guest room inda nan aka jera all kayan amfani birthday din aciki, fitowa sukayi zasu koma sama daidai lokacin aka bude kofa aka shigo, Asad ne yana sanye da wani 3quater na sojoji green da white riga, sai uban kamshi yake zubawa kana ganinshi kasan yay wanka, ganinshi yasa duk suka gaidashi. "Ya Asad good morning" "morning" ya amsa su atakaice yana shigowa cikin falon, sanan ya kallesu yace "the 3 of you should go to my flat and clean everthing now, kuyi mopping" gyadamai kai sukayi dasauri babu gardama duk suka wuce dudda sunada abinyi, ahankali yahau stairs din yana tafiya ahankali yashigo falon sama yanason yaje yagaida Ammi yabata hakuri finally su shirya dan yagaji da yanda ta share shi ko nemanshi batayi, muryan Turai yaji tana magana awaya zata bude kofan dakin datake ciki tafito hakan yasa yatura kofan dakinsu Rahima yashiga da sauri daidai tana bude nata kofan tana fitowa yana rufe kofan batare daya bari yay making any sound ba, dawani irin sauri takira sunanshi tace "Asad" dakin yashigo dasauri yana kalle kalle ya tsani matar nan baimason hanya tahadashi da ita ko kadan, ganin wardrobe dinsu yasa yawani irin bude yashiga dasauri ya labe ciki dan yasan dole tashigo tanemai daidai lokacin Du'a tabude kofan bathroom tafito daure da pink towel din datagani abayin akirji tana kalle kalle to wani kaya zata saka yanzu, gaban wardrobe dinsu tayi ta tsaya sanan takai hannunta ta bude wardrobe din ido da ido sukayi da Asad daya ware idanunshi dan yazaci Turai ce, daidai lokacin yaji muryan Turai tana kokarin murza handle din kofa tace "ba takadirin yaron nan nagani yanzun nan yashigo dakin nan ba" hannu yasa yawani irin fizgo Du'a tashigo cikin wardrobe din zuwa jikinshi sanan yasa hannu yajanyo kofan wardrobe din yarufesu daidai Turai ta shigo dakin, wani irin matse Du'a yayi ajikinshi yana daura yatsunshi akan bakinshi murya chan ciki yace mata shiiii alamun kartai ihu ko any motsi. Bin dakin Turai taida kallo wayan nakan kunnenta tace "I thought shina gani ja'irin yaron nan fitsararre, wlh duk family mu babu wanda ya rainani irin Asad" saikuma chan taja tsaki tace "halan mugun haushinshi danikeji yasa nake ganin abubuwa kaman shi, sukuma ina yaran nan duk sukayi suka bar daki haka kaman na mahaukata, daki kacha kacha kaman ba na yan mata ba" tai maganan tanabin komi nadakin da kallo. Runtse idanunta tayi gam jin jikinta gabaki daya acikin na Asad hannunshi daya na waist dinta dan tanan yarikota dayan kuma nakan lips dinshi dayamata alamun tai shiru tana shakan wani irin mugun kamshi dayakeyi dake sa jikinta yana wani irin saki kaman tanajin bacci, ga kamshin numfashin shi dake fita yana sauka akan jikinta, wani irin sanyi taji tanaji heart dinta na beating way too fast, jin karan bude kofa tafita yasa yasauke ajiyan zuciya ahankali yana kallon fuskan Du'a data runtse idanunta gam gam ko'ina najikinta narawa, dan sakon wardrobe din akwai ray na haske dake shigowa dake haskata saisa yake iya ganinta da kyau, sosai ta runtse idonta gam gam lips dinta nawani irin rawa yana feeling yanda zuciyata ke bugawa da sauri da sauri sabida yanda take jikinshi, zufa dayaga tanayi agoshi yabida kallo zuwa wuyanta, she looks so cute and helpless a hannunshi, baisan maisaba kasa sakinta yayi dudda yaji Anty Turai tafita daga dakin, murya chan kasa ta yanda dagashi sai ita zasu iyaji yace "Ke" bude idanunta dasukai dan ja tayi tsabagen yanda ta kankamesu tadaura akanshi tana kallonshi cikeda mugun shakkan shi, cikin wanan fuskan nashi nababu alamun wasa aciki yace "are you scared"? gyadamai kai tayi ahankali kaman yar baby shi idanunta na neman kawo kwalla, murya chan ciki still batare daka gane yanayinshi ba yace "of what"? lips dinta narawa sosai kaman wata yar baby tace "of you and her" tanuna mai kofa alamun Anty Turai danta lura matan batada mutunci her face alone is not welcoming, cikin wata irin murya kaman batashi ba yace "kinsan dama tana aikin yan yankan kai tana saida yara ma yan shan jini that's why nima nake tsoronta, nabata ke takaiki gidan yan shan jini su kasheshi"? Dawani irin sauri ta girgixa mai kai hawaye sharrr ya zubo daga idanunta dan he sounds so brutal zaka dauka da gaske yake, yana kallonta still yace "hold me tight to inba hakaba zan bata ke takaik......" baikarasa maganan ba tawani irin kankameshi da kyau ta chusa fuskanta akan kirjinshi tana kuka ahankali jikinta ko'ina narawa, wani irin lumshe ido yayi yana having one kind strange and awkward feeling dashi kanshi baisan nameba, shakewa muryanshi yayi ahankali yace "Ke" dago jajayen idanunta tayi daga jikinshi tadan kalleshi atsorace, da shanyayyun idanunshi yana kallonta yace "mubace daga nan karta ganmu"? Gyadamai kai tayi dasauri tana share hawaye da bayan hannunta, lumshe ido yayi yabude ahankali yasake daurawa akanta yace "close ur eyes zanyi wani abu dazaisa mubace daganan kome zakiji don't open ur eyes idan kika bude zan turaki waje sanan inyi ihu infadama kowa ke kika jawoni dakinku harda sani a wardrobe dinku sanan Anty Turai takaiki gidan shan jini, now close ur eyes" dawani irin sauri ta runtse idanunta gam gam tana jikinshi, shi kanshi baisan wani irin evil spirit ne yashigeshi ba, kirjinta yabida kallo data daura pink towel akai, towel dinma yadan zame yay kasa kadan dan yana ganin saman cikakkun tsayayyun boobs nata, yabi neck dinta da kallo dake jike da zufa dan babu iska ko kadan a wardrobe din gashi kuma tsoron datakeji dayasa takw kara keto uban zufa, ahankali yajuyarda ita ya mannata ajikin bangon wardrobe din shi yanata gabanta fuskanshi yakai saitin wuyanta gently yahura mata iska akan wuyan wani irin yirrrr taji dayasa lips dinta yafara rawa sabida iskan saiyasa taji wani sanyi akan zufan datake ketowa, ahankali yakai babban yatsanshi yadaura kan lips din yana murza lips din dake rawa sanan yasaukar da kanshi kan wuyanta yana shakan kamshin datake yana wani irin shinshinata hancin shi na gogan skin dinta sanan yadago kanshi ahankali yana kallon lips dinta dayake murzawa da yatsunshi still, cire Yatsun yayi sanan ahankali yana wani irin kallon fuskanta da yanda ta runtse idanunta gam gam dake pulling nashi more ahankali gently kaman wanda baiso yayi yadaura lips dinshi kan nata, wani irin bude idanunta tayi kaman ankunna globe w din wutan lantarki hada ido sukayi dashi da idanunshi dasuka kankance kaman bashiba kafin gently yamaida nashi idanun ya lumshe ahankali yakamo duka lips dinta da kyau yashiga kissing yana wani irin sauke ijiyan zuciya kaman yadade yana neman abin bai samuba. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR EPISODE 3️⃣9️⃣ Tunda take yau shekarunta dai dai har ashirin da daya dayan watanni aduniyan nan bata taba sanin something like this exit ba, ko Novels din da Ya Hamad ke siyo mata tana karanta anyi kiss but ba'a taba explaining abinda akeji a kiss dinba, danji tayi gabaki daya duka gabobin jikinta sun dena aiki idanunta kur har lokacin tana kallon fuskanshi yanda yake kissing mouth dinta passionately kaman he has been waiting for the kiss for a very long time, yakankameta sosai yana nishi sosai making some wired sounds tsabagen yanda kiss din ke tsagamai kai, hannunshi nashafa gefen fuskanta zuwa kanta ribbon din data kama gashin dashi yawani jaaa yasaki gashin yana tura hannunshi dayaji yana nitsewa ciki silky hair din yana wani irin nishi mai kama da sambatu amman ahankali yana kara barbaza kitson yana yamutsa su. "ahhh....unnnn......huhhhh" sauko da hannun nashi yayi yana shafa wuyanta ahankali tunda yake baitabajin fata mai taushi irin nataba wlh jikinta zaima iyafin na jariri taushi ahankali yakai hannunshi saman kirjinta tasaman towel din batare daya matsa nonon ba ko damko suba feeling how big they are, rawa sosai hannunshi yashigayi kaman anjona dawani abu soyake kawai ya fizge towel din ya yar ya tumurmushe boobs din yasha amman yana kokarin hana kanshi hakan yasa yaki motsi da hannunshi trying to fight the temptation kawai ya ijiye akansu ne yana wani irin tura bakinshi cikin nata ahankali yafara dunkule hannun zai matsa kawai yaji muryan su Rahima dawani irin sauri yasaki bakinta tareda komawa baya da sauri yana kallonta saikuma yabude kofan wardrobe din yafito da sauri gabanshi yamugun tashi dayasa yakalli gaban wandon cikin wani irin kunci yace shit, hannunshi yasa ciki ya gyarata tahanyar mikota sama daura wandonshi akanta sanan yay hanyar kofa daidai suna budo kofan, daure fuska yayi yanuna dakinsu yace "why is dakinku so dirty haka"? duk sunnar da kansu kasa sukayi, cikin fushi yace "karna dawo dakin nan baku gyara shi ba" sanan yasakai yafice dakin Ammin shi yayi harda gudu gudun shi yana shiga yamaida kofan yarufe ganin bata ciki yasa yafada kan gadonta yanajan bargo yay wani irin wahalallen nishi yana mika aahhhhhhhh sanan yakankame kanshi idanunshi sunyi jajir. Yana wucewa duk suka shiga dakin da saurin su Aneesa tace "ina Du'a damuka bari zata shiga wanka" dasauri Rahima tai bayi ganin babu kowa ciki yasa tace "babu kowa" ganin kaman kofar wardrobe nasu abude yasa Mariya tai wajen dasauri tabude saita tsaya turus tana kallon ciki, ganin haka yasa duk sauran sukazo duk suka tsaya Du'a suke kallo dake tsugunne daure da towel akirji takife kanta akafa sai uban zufa take karta a sake yana taba har kasan wardrobe din, kallon junansu sukayi saisuka kwashe da uban dariya dukansu Mariya tace "yanzu sabida Ya Asad kika labe a wardrobe jibi yanda kike uban zufa" dago kanta tayi ahankali lips sunyi pink yirrrr sunwani kumbura sabida yanda ya tsotse su idanunta sunyi ja sabida kukan datayi" dasauri Aneesa gabanta hannunta takai tana sharemata hawaye tace "wai haka kike tsoron Ya Asad jibi yanda kikai kuka har idanunki da lips dinki sun kumbura, babu abinda zai miki wlh, ko munan baya dukanmu shi kawai baruwanshi da yarane, sorry kinji, tashi ki wanke fuska a ayi kizo nabaki abayan dazakisa mutafi" Aneesa tai maganan tana dagota, Rahima tace "Mariya zomuyi sauri mu gyara dakin nan kiga" gyara dakin suka shigayi itakuma tashiga bayi ahankali ruwa takunna ta tara hannunta ta wanke fuskanta sanan tadago kanta takalli madubi abinda yafaru ne yanzu just flash a mind dinta dasauri tadauke kai tafito duk ta zama so uncomfortable, shiryawa duk sukayi suka fito, Ammi duk suka gani afalon sama da Anty Turai sukace "Mum muntafi" "a dawo lpy ai gashichan duk sun cikamana gida da decoration wai ahaka ma basu gamaba" cikeda jin Dadi Aneesa tace "ai Dad is the best, kumu tafi, Ammi bye" binsu da kallo Ammi tayi barin Du'a dataga idanunta sunyi ja kaman ta tambayeta mesa idanunta sukai ja saikuma ta share ganin Anty Turai awajen ta daga musu hannu suka tafi, sanan ta tashi tace "bari kiga na leka dakina tun tuni ina dakin Baban su ina gyarawa" tai maganan tanayin hanyar dakinta, ahankali tasa hannu tabude kofan dakin Asad tagani kwance kan gadonta yarufa da bargo yana bacci, fuskanshi kawaine abude yana zufa dudda uban AC dake kunne adakin, maida kofa tayi dasauri tarufe takaraso dakin, zama tayi abakin gadon tana kallonshi kafin ahankali takai hannunta saman kan goshinshi taji zafi amman zafin na cooling down ne saisa yakema zufa, ajiyan zuciya tasauke ahankali rabonda tasashi a ido tun jiya da Babanshi yadawo, tai bala'in kewanshi but kawai ta shareshi ne sabida ya gyara kuskuren shi dan bakin halinshi yayi yawa inma haka tamaiba zai karama yar mutane haka, tana zaune awajen tana gogemai zufan harya farka around karfe biyu, bude idanunshi yayi ahankali yasauke akanta dasauri tace "imaza kajeka shirya katafi jummaa naga bakada lpy ne daman saisa bantadaka ba" gyadamata kai yayi ahankali yana tashi zaune, saikuma ahankali yatashi tsaye takalmanshi yazura yawuce yafita, hanyar stairs yayi yana sauka Anty Turai na fitowa daga ciki, kafinma yay magana tace "ni daman nasan naganka wlh dazu dan banyi tsufan da za'ace bazan ganeka ba Asad idan na ganka" tai maganan tana ijiye kulan data dauko kan table sanan ta taho inda yake atsaye yana kallon gefe ahankali yace "ina yini Anty" cikin fushi tace "har yanzu dai Anty nan bazai fita daga bakinka ba yau kwana na nawa agidan nan" ahankali yace "biyu" wani mugun kallo tamai tace "shine saiyau kake gaidani shima dan mun hadu, wuce katafi nasan maganinka agidan nan nine daidai dakai wlh" kaman jira yake dasauri yawuce tabishi dawani bakin harara. Sai wuraren 4 suka baro shagon Hudayya kowa rikeda hadadden dress dinshi, around 5 suka dawo, da kyar sukabar Du'a ta tafi gidansu shima dan sunga dagaske take dan koda sukaje shagon Hudayya tai shiru duk tai wani irin sanyi tana shiga a falo ta yarda jakan kayan tawani irin fada jikin Grandma dake zaune tana waya tai shiru, saida Grandma tagama sanan tadubeta tace "Ya akayi Yammata na" murmushi tayi tace "Grandma nagaji" dariya tayi tace "su Aneesa basusan ke baki saba da irin gantali gantalin nan bane, sannu" lumshe ido tayi tace "Grandma zanyi bacci 6 saiki tadani" shafa fuskanta Hajiya tayi tana kallonta tace to, lamo tai jikin Grandma tanajin natsuwa she really needed this, dan tundazu ba'a natse takeba tarasa mezatayi tadaina tunanin abinda Asad yamata abu kadan sai takai hannunta ta taba bakinta ahaka bacci yay awon gaba da ita. 6 daidai Grandma ta tadata da kyar ta farka sama tawuce tai wanka sanan tai salla tana zaune kan dadduma tai isha'i sanan ta tashi da sauri jin Grandma na kwala mata kira dasauri tacire hijabin tasauka kasa da gudu Mariya tagani taci gayu sosai anmata makeup tareda wata mata da Grandma, tana ganin Du'a tace "hope kinyi wanka duk mun shirya fa mai makeup nakawo tamiki naki" gyadama kai tayi batare datai magana ba, Grandma tace "jeki zauna to amiki" zama tayi aka fara mata makeup din Grandma ta tashi tawuce sama tana waya Du'a nabinta da idanu dan daga gani wayan kind of seems serious. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR EPISODE 4️⃣0️⃣ Da aka fara mata makeup din ita kanta Mariya waje tasamu kan kujeran dake facing nasu tana kallon Du'a, wato hakika tsarki ya tabbata ga ubangijin daya Hallici yarinyan nan, takalli Du'a, takalleta takara takalleta dan tanemi nakasun yarinyar in term of hallintanta amman babu, abunku da wacce bata taba makeup ba saitai wani kalan kyau da duk wanda zai kalleta saiya sake kallo, saida aka gama tsaf mai makeup din tace "jeki saka kayan saiki sauko mu gyara gashin muyi styling gashin gaban kan nan naki" tashi tayi Mariya tabita da sauri sukai sama, bude jakan huddayan tayi taciro wani hadadden black gown da akayishi dawani silk material saidaga tawajen wuyan da kirjin da hannun kayan aka yisu dawani net lace dake wall wall mai duwatsu, sakawa tayi Mariya tajamata zip tabaya rigan baiwani kaimata kasa chan ba saita dawo kaman wata cindarella, kallon gaban rigan tayi yanda ake ganin alamun boobs dinta sabida yanda yataso yasa takalli Mariya kaman zatai kuka tace "jibe fa ana ganina bazan iya fita ahaka ba" dasauri Mariya tace "dalla ke Du'a nan kin cika kauyanci baga nawa ba gana Ya Rahima duka iri daya fa aka mana, boobs dinki basu fitowa wlh sabida kawai kinfimu boobs ne yasa suka taso kikaga kaman ana ganin ta net lace dinan ne" sauka muje amiki head saikisa takalmin ki" bata jira amsanta ba takama hannunta suka sauka kasa ita kanta mai makeup din saida tace "masha Allah kinyi kyau, bari ayi daurin" wani simple modest dauri tamata dayama kanta kyau sosai, sanan Mariya yabada wasu silver dankunne aka samata wow, saiga hill din mai wasu irin silver stones haka, samata akai akafa, kafanta kadai ka kalla saikaji kaman kaci wow, sama Mariya ta tafi tafito da turarukan ta tafesa mata sanan ta ijiye turaren awajen tace "tashi muje" tashi tayi tana kallon kanta feeling so uncomfortable dayasa Mariya taso a dariya ta fizge hannunta tace "wlh bazaki ja afara bani ba" hakanan tabita suka fita compound sai lokacin ma sukaji kida natashi alamun anfara, tsayawa Du'a tayi tana kallon kanta tace "gyale fa" "gyalen me ga gidanmu ga naku muje jor" tanaji tana gani Mariya tajata haka suka fita, gate din gidansu sukayi dayake abude zaka dauka rana ne sabida yanda ko'ina wuta bauu gawani maddd decoration da akayi na gold da black, ga kawayensu yan Nile maza da mata dasuka cika gidan ana raye raye ana ganin Du'a aka bita da kallo dayasa tama sauke kanta kasa sabida yanda takeji suka shigo tana tafiya ahankali sai abin yayi kaman wani yanga takeyi, wajen wasu kawayen ta Mariya tayi hakan yasa da sauri Du'a ta tafi chan baya chan tasami wani empty table dake zagaye da kujeru taja kujera daya daga cikinsu tazauna tana kallon yanda yammatan ke rawa abinsu babu kunya. Sasu akayi sutashi lokacin da birthday girl zata shigo ita kanta batagane Aneesa ba dan tai kyau matuka hakan yasa tai wani irin murmushi tadau wayanta zata mata hoto danta gayamusu sumata hoto dukansu, gyaran murya taji anyi abayanta dawani irin sauri tajuyo, Sharif ne yana sanye cikin riga da wando yay kyau sosai sai kamshi yake yana mata wani irin kallo kaman yau yafara ganinta, daidai ance su zauna, janye idanunshi yayi daga kanta yasa hannu ta gefenta yaja mata kujera murya chan kasa yace "sit" zama tayi ahankali tanadan murmushi hakan yasa shima yazauna akujeran kusada ita, wayanshi yabude yashiga camera yakalleta yace "selfie please miss" yanda yay maganan saida yasa tai murmushi tace "kafara ko" posing tayi ahankali hakan yasa yadan matso da kanshi kusada nata sosai yana sha kan wani cool feminine scent datakeyi sanan yay clicking camera din yadauki hoton sanan yakara matsowa kusada ita yace "jibi yanda mukai kyau" gyadamai kai tayi tana kallon hoton, sanan tajuya tamaida hankalin ta kan event din yanda MC ke magana, tundaga kan hannayenta data ijiye kan table din Sharif yake kallo har zuwa fuskanta dayay wani kalan asirtaccen kyau, gashi sai murmushi take sabida yanda take kallon su Aneesa da Rahima dake raye raye abinsu abin yana bata dariya tana wishing inama yan gidansu ne, wani irin bugawa kirjinshi fast fast shi yafara, he wish she's his right now da dakinshi zai tafida ita, her happiness is infectious daji yayi kaman yadauketa subarnan wajen yakaita wajen da she will even be more happier than ever, hakanan tayi ajikinta ana kallonta hakan yasa tajuyoda sauri hada idanu sukayi dasauri yadauke kai yana murmushi yace "ohhkay she caught me" yadan lumshe idanu sanan yabude yajuyo da kanshi yakalleta yace "kinyi kyau ne saisa nake kallonki" dan murmushi tayi tasake juyarda kanta tana kallon Aneesa dake rawa da Mum dinta dinan dabata ma mutane murmushi daman ance yar yankai kai ce, hamma tayi danwani kalan shegen bacci takeji kaman ba itane taina awa daya ajikin Grandma dazu ba, kallonta Sharif yayi ganin yanda tai hamma alamun bacci yasoma zuwa yace "zakiyi manni?" juyoda kai tayi takalleshi dasauri ta girgizamai kai alamun a'a, bandir din yan 500 guda biyu sababbi ya ijiye agabanta yace "dauka ki rike kintashi muje ana birthday na besty ki bazaki mata manni ba, common don't be a bad friend daganan ma saina koyamiki yanda ake rawa" makemai kafada tayi alamun bazata ba, juyawa yayi ya kalli inda suke ganin babu mutane awajen dan dama ba'a fara zuwaba hakan yasa yadauko yana kallon fuskanta yace "koki tashi muje spray money and dance inba hakaba I will be honorably glad nadaukeki akafadana after all kinyi kyau sosai, so all eyes zai dawo kanmu, tashi and pack ur money" yay maganan looking serious tashi tayi ahankali tareda daukan kudin tana turomai baki dan yadameta, atare suka jera yana tafiya da ita ahankali ganin da kyar take tafiya da hill din kafanta, Aneesa na ganinta tawani rungumeta tana rawa tace "common dance with me best friend" kasa rawa tayi tana murmushi sabida yanda duk ake kallonta, tace "ni kudi zan manna miki" washe baki Aneesa tayi tasaketa tana mata rawa da kyau dan taji dadin mannin, kudin tafara manna mata batare data bari sun hada ido da Anty Turai ba dake gefe tana rawa da wasu manyan mata friends dinta dasuka zo, sosai taji she's feeling somehow a filing dudda Sharif na gefenta yana mata manni ita tana mannawa Aneesa, rasa abinda yasa she's is just feeling uncomfortable yasa ta waigo da kanta tanama Aneesa manni still tanabin kowa da kallo dake filin rawan, dake zaune kan kujeran kafin ahankali idanunta su sauka kan Asad dake tsaye wajen parking space dinsu da babu motoci awajen dan duk anfita dasu waje yana sanye da 3quater wanan karan black da riga mai kyan gaske mai ruwan toka dabai saka boturan kirji ba hannunshi rikeda glass cup yana sipping non alcoholic wine daya karba awajen bar man na party, hada idon dasukayi yasa taji kafanta yawani turgude hakan yasa hill din yaturgude shima tai baya zata fadi dasauri Sharif dake gefenta yatarota batare daya riketa ba amman da jikinshi yahanata fadin bakinshi yakai saitin kunnenta yace "easy Pretty it won't be nice kifadi awajen nan bayan kinyi kyan nan all eyes na kanki" tashi tayi daga jikinshi tayida sauri tanadan murmushin yake tacigaba da manna ma Aneesa kudin data kosa su kare dan tagaji da manna su bata kara yarda ta kalli inda taga Asad ba, daidai lokacin Dad dayaci manyan kaya tareda Ammi suka shigo filin hakan yasa Sharif yaja hannunta gefe da sauri ta kalleshi murmushi yamata yana sakin hannunta yace "lemme dance for the pretty gurl oh yes yimin manni" rawa yahau mata yanabin wakan he looks so cute and funny dayasa tama hau dariya, Mariya ce ta taba Rahima tana nunamata da baki kalli Sharif da Du'a , murmushi tayi bayan ta kallesu tacigaba da rawa abinta, manni Dad da Ammi sukahau yima Anty Turai, sanan Dad tajuyo zaifarama Aneesa dake taredasu Rahima manni idanunshi suka sauka kan Du'a dake dariya sosai tanama Sharif manni dake mata rawa harda dan tafinta, kallo daya yamata yaganeta dan image dinta yakasa goguwa a memory shi, Sharif dake rawane yalura da kallon da Dad kema Du'a dan yanda yake kallon Du'a ma yasa yakasama Aneesa mannin, dasauri yace "muje ki gaida Dad dinmu Du'a" juyawa takalli Dad dayake nunamata dake kallonta ko kadan bataganeshi ba to ranan ma wani kallonshi tayine, ahankali tace "ina yini" kasa amsa gaisuwan ma Dad yayi sai kallonta dayakeyi hakan yasa Aneesa dasauri tamatso takai bakinta saitin kunnenshi tace "Dad she's my best friend danake gayamaka Du'a jikan Hajiya ce, Dad tanada kyau ko" wani irin washe baki Dad yayi yana kallon Du'a from head to toe yace "sosai ma, I like what I see" yay maganan yanadan cizan lebe, sanan yace "dance for me fine girl namiki manni" yay maganan yana fara mata manni yana wani irin kallonta dayasa Sharif yace "tabar wayanta achan muje ki dauka" baijira amsan taba yaja hannunta suka fitadaga filin suna tafiya Sharif nagaba tana biyedashi abaya Dad nawani irin binta da kallo kaman wuyanshi zaicire ganin hips masha Allah dominkam Allah yamata ass, curvy and bumpy. Inda suke dazu suka koma Sharif yajamata kujera ta zauna sanan yazauna kusada ita wani abu namai wato aranshi, daurewa yayi yadanne ya matso kusada ita sosai ahankali yana kallonta yace "Du'a" kallonshi itama tayi tace "uhm" ajiyan zuciya yasauke yasaukar da idanunshi kan fararen hannunta sanan gently yamika hannayenshi biyu yakarbi hannunta yarike dasauri takalleshi, dan murmushi yayi batare daya kalletaba yana kallon hannun yace "sorry nasan na rike hannunki kuma ba kyau I just wanna tell u something ne" yaydan shiru sanan ahankali yace "tun ina dan yaro nakanyi mafarki na auri mace irinki" yaydan shiru sanan ahankali yace "inason mace mai natsuwa da aji, ni namiji ne dako kadan wayan nan wayayyun matan yan gari da sauransu basa burgeni hasalima nafison mace wacce batasan komiba wacce nice zan shayarda ita dadi nakoyamata komi, mai natsuwa mai kyau kamila mai cute smile, ranan dana fara ganinki I saw that kind of lady in you, I love you so m....." tsayarda maganan yayi jin fuskarta akan hannunshi, dasauri yakalleta bacci tayi. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR Not edited sorry banyi editing this page. EPISODE 4️⃣1️⃣ Zaiyi magana saiga Rahima ta taho wajen tana murmushi tana kallon Sharif irin kallon nan na nasan komi daure fuska yayi tana karasowa gabanshi yace "me" dariya tayi tace "babu naga tayi bacci ne shine zan tadata muje chan dakinmu ta kwanta tunda kasa ce ita" hararanta yayi yace "come amman kibita ahankali please wlh duk kun wahalar da yarinyar nan ita batasaba da gantali irin nakuba" tabe baki Rahima tayi tace "cute Baby alert wlh harna hango d'anda zaku haifa" tai maganan tana tapping fuskar Du'a tana kiran sunanta Du'a, Du'a, bude idanu kadan tayi hakan yasa Rahima tace "tashi muje ciki nima fitsari nakeji" mikewa tsaye tayi dasauri duk cikin bacci tana sosa ido, wayanta Rahima tadauka tace "muje" gaba Rahima tayi hakan yasa Du'a tabiyota abaya ahankali tana tafiya kadan kadan danga bacci gakuma takalmi Sharif yabita da kallo baccin dayagani a idanunta yasa baice mata komi ba, bude kofa sukayi suka shiga falo sama sukayi suna kaiwa dakinsu Rahima kawai fadawa gado tayi ko lafiyayyen 1min batayiba bacci yasakeyin awon gabada ita, itakuma Rahima tawuce bayi fitsari tayi sanan tafito tana kallon yanda Du'a ke bacci ko takalmi ma batacireba tace "Allah sarki Du'a aikam kingaji wanan bacci haka, fitinan Aneesa kadaima yaci kimai baccin nan yau kwana nawa tahana mutanen gidan nan sukuni da shegen birthday dinan" tai maganan tana daura hannu akan switch takashe wutan dakin tawuce tafita sanan tafito ganin Sharif yakoma filin rawa yasa tace "yagama soyewa yakoma rawa kuma" murmushi tayi tawuce wajen itama duk abinda ke faruwa a idanun Abba, ahankali yazame jikinshi yasudade yawuce flat dinsu batare dakowa yalurada shi ba. Sama yayi dasauri kirjinshi na beating fast fast, direct dakinsu Rahima yayi yabude kofa ahankali kaman barawo, ganin dakin da duhu yasa ahankali yakai hannunshi kan switch din wutan dakin, kunna wutan dakin yayi dakin yay wani haske bau, ganin Du'a kan gado tana bacci yasa da sauri yawani irin waiga baya yana kallon falon saman su jin shiru babu wanda yakenan acikin gidan yasa yamaida kofan yarufe ahankali sanan yasake waigowa, tundaga kan kafafunta dabata cire silver hill dinta ba yake kallo dasukamai bala'in kyau zuwa kafafunta dasuke abude sabida daman rigan bai kaimata har kasaba gashi yanda ta kwanta yasa yadan kwashe gefe sai faran kafanta ya bayyana harzuwa wajajen bayan gwuiwanta, wani irin lashe miyau bakinshi yayi jikinshi har tsuma yake yace "wanan wace irin danyar yarinya ce haka, yarinya kaman hurun ini, Ya ilahi jibi fata saikace da jinin dawisu take wanka kullum wayyo Allah na gabana" yay maganan yana takawa zuwa gefen gadon yana wani irin kallon fuskanta da gaban riganta dayasa yanayin kwanciyan ta kirjinta yadan fito, wanan karan harwani zazzago harshe waje yayi kaman dan kare yana kallonta baisan lokacin daya mika hannunshi zai tabataba yaji anbude kofan dakin dawani irin sauri yakoma baya gabanshi nafaduwa sosai yakalli kofan Asad yagani da headphone makale akanshi hada ido sukayi da mahaifin nashi, saikuma ahankali yajuya yafice dawani irin sauri yace "shitttt nima maiya kaini, na kwafsa wlh" yay maganan dasauri yajuya yafita, ganin Asad zaune kan kujeran falon sama yana daddanna wayanshi yasa yay wajen yasami gefenshi yazauna yana sauke ijiyan zuciya yace "Asad wacece wanchan yarinyar wai nashiga dakinsu Rahima naduba yama sunanshi gorona dan nemanshi nake naganta kwance tana bacci wacece ita" batare daya kalli Baban nashiba yace "I don't know her" dan murmushi yay yace "kai daman dababu ruwanka da yan gidan nan wama zaka sani" yay maganan yana murmushi yana kallonshi ganin Asad ba kulashi zaiyi ba yasa yatashi yay dakinshi daidai Mariya nahayowa falon saman da gudunta, hada ido dasukai da Asad dake mata wani mugun kallo yasata rage gudun murya chan kasa tace "sorry Ya Asad I'm about to pee on my panties ya matse ni" dauke kanshi yayi yace "when u go inside wake that girl ta tafi gidansu" gyadamai kai tayi batare data iya magana ba dan fitsarin ya matseta tawuce tashiga dakinsu tana fitowa tashiga tada Du'a da kyar ta iya tabude idanunta takalli Mariya, Mariya tace "sannu da aiki Du'a wanan ne birthday ko to tashi kutafi gida dare yayi, fara zuwa ki wanke fuskanki" ajiyan zuciya ta sauke cikin bacci sanan ta tashi ahankali zaune takai kusan 2nin ahaka Mariya tace "kefw nake jira" tashi tayida kyar tashiga bayinsu fuskanta ta wanka fuska sanan tafito tana hamma, wayanta da Mariya tadauka tabata tace "muje" tana gaba Mariya na biyeda ita abaya tana sosa idanu tabude kofa tafito, hada idanu tayi da Asad dayasa taji ta turgude tai baya zata fadi dawani irin sauri Mariya tariketa tace "subhanallahi ke Du'a wai haka kikeda bacci karki fadi kiji ciwo fa" tai maganan tana dan turata sabida ta tashi tsaye da kyau, tashi tayi tasauke kanta kasa tawuce tai stairs batare datasake bari sun hada idanu ba. Har gate dinsu Mariya tarakata sanan tadawo ahankali tabude kofa tashiga falonsu tana tafiya babu kowa falo tariga tasan su Razika sunyi bacci stairs tayi tahau tun kafin takai karshen stairs din takejin muryan Grandma nafada, mamaki abin yabata to dasu Razika take fada, but hardly kaga Grandma nama su Razika fada dan bama su cikamata laifi ba, tun tanajin hayaniya fadanta bata jin maganganun datake tana kaiwa falon sama tasomajin maganganun da kyau. "Muhammad nagayamaka ka kira kanwarka ka shaida mata wlh inhar tazabi mijinta kanni mahaifiyarta dana haifota duniya na shirya na yafe Zainab, tasha min laifi I ignore nahakura I always term abubuwa da kuskuren datakeyi amatsayin soyayya ce tarufe mata idanu but nalura abin mata tsabagen iskanci ne, kagaya mata maganan Du'a tadawo karta karamin shi inba hakaba wlh wlh wlh saina masifaffen bata mata rai"...... iyanan taji kawai taji gabanta na mugun faduwa, tana ganin tunda tazo gidan nan bata tabajin Grandma nafada tana masifa ba sai yau, Du'a tadawo! Du'a tadawo! komarda ita kano za'a sakeyi, nooo jitayi kanta yawani irin buga yasara dasauri tajuya takoma kasa, kitchen ta shiga tadau ruwa tashiga sha dasauri sauri, wani irin shakewa tayi hakan yasa tasaki cup din kasa tana tari sosai tana bubbuga kirjinta, Grandma ta fitowanta daga daki kenan ranta abace jin tari yasa tasauko dagudu tayo dinning gani Du'a a kitchen ta dafa fridge tana tari sosai idanunta sunyi ja yasa tace "subhanallahi sannu sannu, daga shigowanki sai tari Du'a, halan kishi ki kije sosai, sannu ko" tai maganan tana bubbuga bayanta, tsayawa tarin yayi Grandma tace "sannu, iyye daman haka akasha kyau yanmata ko a nunamin aka wani tafi, ya akayi kika dawo naji ba'a gamaba" asgaeabe tacd bacci nakeji, fuskanta Grandma tashafa tace "jeki kwanta to kinji, amman ki wanke wanan fentin da aka miki kafin ki kwanta kinji yar albarka, Allah yatashemu lpy" gyadama Grandma kai tayi tana tafiya sama hawaye ya zubo mata Grandma tabi bayanta da kallo cikeda wani irin so dan sosai Du'a tashiga zuciyanta yanda yarinyar nan ta zama happy girl gashi harya making friends bazata taba bari tKoma kangin datake ciki daba wlh. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 4️⃣2️⃣ Yau dakanta ta tashi da Asuba sabida batama iya tai baccin kirki ba tunda taji wayan da Grandma keyi, koda Grandma tashigo taganta akan dadduma murmushi tayi tawuce tafita daga dakin, tadade kan dadduma sai wajajen 8 tafito da safe, ahankali tabude kofan dakin Grandma ganinta zaune kan gado yasa tashiga ciki tamaida kofa tarufe tana murmushi takarasa wajenta tace "Grandmaaaaa dina, good morning" hararanta Grandma tayi tace "daga zuwa birthday party sai bacci kai Du'a" dariya tayi sosai batace komiba, Grandma tace "oya sauka kasa kiyi kari saikije ki shirya yau malaminki zaizo" sauka tayi dagakan gadon tace " to" juyawa tayi tafita daga dakin, breakfast tayi tanayi tadawo sama sanan tai wanka tashirya 10 nayi malamin ta yazo, hadda tabashi shi karan kanshi malamin yanda yaga takeda kwazo dakuma kokari yasa saida ya yabamata, karfe 1 suka tashi fitowa tayi tana tafiya tun kafin takai falon takejin hayaniya, da Sallama tabude kofa tashiga Ammi tagani tareda Dad da Grandma duk zaune a falo suna hira, suna ganinta duk suka bitada kallo hakan yasa cikeda kunya tadan duka tace "ina yininku"murmushi duk sukamata Ammi tace "har an tashi Du'a" gyadamata kai tayi ahankali, Ammi tace "to Allah bada sa'a, tai sama abinki ki huta" sama Du'a tayi Dad yabita da kallo yace "yanzu wanan yar Zainab ce Hajiya, lallai Allah mai iko, ni inda acema yar Muhammad ce zan iya na'am da abin duba da shi achan kasashen turawa yake, yarinya gatanan jazur kaman balarabiya" murmushi Grandma tayi tace "wlh yar Zainab ce" dan gyaran murya tayi tace "babu abinda yakai kwanciyan hankali da zaman lpy da iyali Baban Asad, Ammin Su told me everything, Allah ubangiji yamuku albarka Allah yabarku tare" washe baki yayi yana murmushi yace "Alhamdulillah, yanzu sai yan wajenki Asad da Sharif sunakeso yanzu suyi aure" murmushi sosai Grandma tayi tace "zasuyi" sosai sukasha hira, bini bini Dad idanunshi nakan stairs har addu'a yake Du'a ta sauko koya kara ganinta amman bata sauko ba haka wuraren 4 suka tafi. Monday! Wuraren 7:49 nasafe tafito ashirye tana sanye dawani bakin abaya plain black mai flowers bakake, saukowa kasa tayi tana rikeda jakanta a hannun, sahun tafiyanta da Grandma dake cin dumamen tuwo taji yasa dasauri tadago kanta ganin yasa tace "Yammatan nawa ne haka har anfito" wani irin murmushi tayi arayuwa ayanzu jitake batada wanda takeso kaman Grandma tace "Grandma nima zanci dumamen" gyara zama tayi tace "Alhamdulillah zokici zanma iya barmiki idan zaki cinye" dariya tayi tasa clean hand dinta tafaraci tana kallon TV dake aiki, Grandma tace "kibar office dinan yau gobe sai ki fara, sai anjima da yamma za'a kawomin abubuwan ki, banson ki saba dokan Asad ne" dasauri tace "yauwa Ammi namaje wajensu Aneesa" hararanta Grandma tayi cikeda wasa tace "sannu uwar yawo angulu" dariya tahauyi Grandma ta harareta tace "ci abinci kafin na makeki awajen nan" dasauri tacigaba dacin tuwon, Grandma dake kallonta tace "su Aneesa suntafi school yau, kema inaso nakira malamin ki na tambayeshi progress dinki, yanamiki su biology da chemistry da kyau ko tunda kince ke science zakiyi" dasauri tace "eh yanayi ina ganesu amman Grandma maths ne kebani wahala da physics but ina ganewa suma" "duk zaki iya ai AbdulFatah ya iya lesson, zan tambaye shi if u can stand ma waec zan biya miki kiyi this year kome kikeso ki zama Du'a inhar ina raye I will help you achieve it" murmushi tayi ahankali tace "Grandma thank you" "now stop talking ki cinye ingani" Grandma tai maganan tana tashi tai kitchen dan ta wanke hannu..... Akofar Gidan yay parking hakan yasa ahankali tajuyoda kanta takalleshi kaman yanda shima yake kallonta, ajiyan zuciya tasauke ahankali sanan tabude kofan motar tasa kafa tasauko kana ganinta kaga wacce keda damuwa sosai bude gate din gidan tayi tashiga, security zai tsareta tace "please I don't have time for this, wajen mutane gidan nazo" yanda tai magana yasa yakasa cemata komi tashiga, ahankali tai sallama tabude kofan falon tashiga, Dad ne yana sanye da manyan kaya dan fitowan shi kenan zai fita aiki ganin Asad da yanzu ma yashigo side din yazauna a dinning yana hada coffee yasa yay dinning din, jin sallama da bude kofa yasa atare dukansu biyun suka juyo suka kalli kofan, turus Ammi dake saukowa kasa rikeda hulan Dad tayi ta tsaya, cikeda mugun mamaki tace "Zai.....nab....kece ko gizo idanuna kemin" tai maganan tana saukowa da sauri tai hanyar kofa batai watawata ba ta rungume Mami tace "oyoyo saukan yaushe" tai maganan tana sakinta tajuya takalli Dad da Asad tace "Alhaji don't tell me baka gane Zainab ba Yar Hajiya ce Maman Du'a" dawani irin sauri Asad yadago kai yakalleta, tahowa Dad yayi yana murmushi sosai yace "Zainab ido kanga ido dama bakida zamunci" murmushi tayi na dole saikuma hawaye, hannu tasa tagoge hawayen dasauri zatai magana kuma saita fasheda kuka sosai, dawani irin sauri Ammi tarike mata kafada tace "subhanallahi Zainab menene come, sit" tazaunar da ita kan kujera tana kallonta tace "menene" cikin tsananin damuwa tace "Hajiya nazo wajenku ne sabida nasan Mama zataji maganan ku zata saurareku cemin tayi nazo mata gidama bata yafemin ba, mutanen nan sunaso su karbi yarsu Kakan su ta matsa a dawo da ita gida, nama Mama bayani namata namata taki ta fahimceni, i don't know what to do, Baban Du'a ma na waje" dasauri Dad yace "assha maisa baki shigoda shi ba, je dauko mayafinki Wife mutafi wajen Hajiya" gyadamai kai Ammi tayida sauri tawuce tai stairs tana kallon Asad da kanshi ke kasa kaman baimasan me ake afalon ba, ko 1min batayiba tafito, Dad yace "kutaho to" dagata Ammi sukayi suka fice. Cikin mutunci sosai Dad da Abba suka gaisa sanan yamusu jagora yace "bismillan ku muje" shiga gidan sukayi Abba na gaba, da Sallama yabude kofar falon yashiga, Grandma na zaune kan kujera tasanya glasses dinta a idanu tana aiki a sysyrwm dinta, jin sallama yasa tajuyo, ganin Mami da Abba tareda Dad da Ammi yasa ta ijiye system dinta agefe tamike tsaye zatai magana dasauri Abba ya tsaya agabanta yace "Hajiya aikin daukeni amatsayin danki ko, sanan kina fadi naji, inason sabida ni ki sauraresu dan Allah Hajiya kinji" Mami Hajiya ta kalla da kanta ke kasa takasa hada ido da ita, sai Abba dashima kanshi ke kasa cikeda girmamawa sanan tadauke kanta takalli Dad tace "Baban Asad kasan ina bala'in ganin mutuncin ka and kaman yanda kafadi nadaukeka amatsayin d'ana dan haka listen to me and obey me, kaga mutanen nan biyu" tanuna Abba da Mami tace "inhar maganan Du'a yakawosu gidan nan ai nariga nafadamata awaya, bazan bayarda yarinyar nan ba, Du'a tagama rayuwan datayi agidansu har abada, na gayamata nakuma gayama yayanta Muhammadu yakara sanarda ita bazan bada yarinyar nan ba bazan bayarba" dasauri Ammi ta tashi ganin Hajiya tadauki zafi sosai tace "Hajiya calm down" cikin fushi sosai tace "don't tell me to calm down, sunason yarinyarne suka azabtar da ita, yarinyar dabaya lissafata cikin yaranshi, sun kulle yarinya, Du'a became so depress, sunyi depriving yarinya of her right, na education, bata iya komi an yaa mace ba, bata iya girki ba, yarinya sun maidata doluwa mara wayau, yarinya yar 15yrs yanzu zata iya saida Du'a, sun cutar da Du'a shine yanzu sukeso su dauketa su maidata gida sabida wacce tace akoreta da farko tace yanzu adawo da ita to wlh wlh kura yay kadan afadan giwa" Ammi karan kanta saita taji tsoro tunda take da Hajiya bata taba ganin bacin ranta da bala'intaba sai yau...... Sosai Du'a kejin hayaniya wanda tunda tazo gidan bata tabajin irinshi ba, tashi tayi dagakan gado gabanta nafaduwa hakanan ahankali tabude kofanta muryan Grandma taji dasauri tafito, jin maganganun da Grandma take duk akanta ne yasa tai hanyar stairs din tana tafiya ahankali, hango Mamin ta da Abban ta, da Ammi da Dad, saiga Grandma a tsaye tana masifa sosai yasa taji jikinta yafara rawa, su Mami sunzo su komarda ita, wani irin kuka ne yazo mata dasauri tasa hannu ta toshe bakinta tahana kukan fitowa, saikuma tajuya da gudu tai dakinta kaman mahaukaciya tana wani irin kuka kaman wacce ke hauka, memory gidansu yahau flashing akanta, rawa jikinta yafara sosai tace "no....no oooo" wani irin bude kofan sip tayi jakan goyonta na makaranta sabo da sum sayo ta fizgo kome tagani turawa take ajakan, gyalen abayan dake jikinta tadaura ta yana akanta sanan ta goya jakan tana kuka sosai, fitowa daga dakin tayi tana kalle kalle saikuma tasake komawa dakinta tai wajen window dakin, bude window tayi tana kallon kasa dan abene take, wani irin fashewa tayi da kuka tana goge idanunta da bayan hannu tace "bazan koma gidan nan ba, bazan koma ba, nooo" kawai tahau kan window kaman wanda aljanu suka shiga, runtse ido tayi kawai tai jumping tundaga saman nan har kasa aiko tafado timmm kan grass carpet din dake wajen wani irin bugewa tayi ahannu da kafa amman bata damuba ta tashi tana kuka sosai tana wani irin dingishi tana tafiya da gudu gudu sauri sauri ko kallon maigadinsu batayiba tabude gate tafice, tana fita tawani irin kwasa dagudu rikewa kafanta yayi hakan yasa tai kara, da kyar ta tashi bamatabi takan kakkabe jikinta ba ta kwasa da mugun gudu tana dingishi, Asad da fitowanshi daga Gate kenan da motanshi zashi office lokacin itama tafito ganin tafadi tasake mikewa tana gudu still tana kuka yasa yatabe baki, saka sit belt dinshi yayi ya danna waka yaja motan yana gudu ahankali. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 4️⃣3️⃣ kafin yakai gate din estate dinsu harta wuce tayi titi tana gudu sosai, fita yayi daga estate din yana jiran traffic light abashi go ahead yawuce, kaman ance yakalli side din left dinshi, ganin yanda take gudu tana dingishi tana kuka sosai yasa yadanyi jim kaman mai tunani, maganan Ammi ne yafadomai rai datamai ranan nan what if kanwar kace su Rahima da Aneesa, yatsine fuska yayi ya karya kwana yaja motan dawani irin mugun gudu, saura kiris yabugeta akan titin hakan yasa ta tsaya chak ganin mota yasha gabanta tana goge hawayen fuskanta tana kallon motan dayake tinted dan bata iya ganin naciki, saukar da glass din motar yayi yana kallonta fuskanshi babu ko alamun strictly yace "get in" girgixa mai kai tayi jikinta ko'ina narawa saikuma tafashe da mugun kuka sosai akan titi tace "dan Allah dan Allah kabarni natafi, Dan Allah Dan Allah Dan Allah narokeka Ya Asad" tunda take bata taba kiran sunanshi ba sai yau, jin yanda ake bugamai horn akan titi yasa azuciye yabude marfin motan dawani irin gudu tajuya zata tafi sabida dingishin datakeyi yasa taku daya yayi ya dauketa tana ihu ko kallon mutanen dake titi baiyiba yabude baya ya jefata ciki yay locking car, sanan yashiga gaba yaja motan dawani irin mugun gudu. Wani irin mahaukacin kuka take a motan shi kaman yana yankata, takasa shiru, saida yay tafiya mai nisa sosai sanan yakai wani filin kwalo dake kan titi yay kwana ya shiga dan babu kowa ciki, parking motar yayi awani irin zuciye yabude motan yafito yabude bayan motan hannunshi yasa yawani irin fizgota waje sanan yabugata dajikin motan yasaka mata mugun tsawa. "shut up!" ko tari bata karaba gabaki dayan kukan datake daya kusan taushemai kunne hadiyeshi tayi jikinta na bala'in rawa, rasa yanda zatayi yasa kawai saita zube agabanshi tai kneeling looking so helpless and pitiful da zakaji kaman ma kamata kuka, kaman karaman yarinya harwani jiniyan kuka take cikin muryan bala'in tsoron shi tace "Ya Asad dan Allah kayakuri kataimakeni allow me to run, dan Allah Ya Asad karka bari su komar dani kano, dan Allah karka bari su komardani kano, dan Allah dan Allah dan Allah ya Asad dan Allah karka bari su komarda ni kano, dan Allah kataimakeni" yanda take rokonshi jikinta narawa kanta akasa dan tsoron shi ma yahanata ta kalleshi yasa yabitada kallo saikuma yay shiru still kallonta yake, yakai kusan 1min ahaka bazaka taba iya tantance yanayin shi ba yace "stand up" tashi tayi tana sauke ijiyan zuciyan kuka tana kuka, gaba yabude mata yace "shiga ki zauna" shiga tayi batare datai musu ba ta zauna, maida kofan yayi yarufe sanan yazagaya ta side dinshi yabude yashiga yazauna yadade yana kallon filin kwallon yanajin yanda take rera kuka ahankali tana sauke ijiyan zuciya sanan yajuyo ya kalleta yanda riganta yay budu budu duk kasa sabida faduwan datayi, dauke kanshi yayi yamaida gefe yana kallon filin kwallon yace "maisa bakison komawa gida" kaman jira take tafashe da kuka tace "Abban mu baya sona, Mum bata sona, su Ya Hawwa da Ya Nana duk basa sona, Kakan mu bata sona,Ya Hamad kadai kesona agidan" murya chan kasa batare daya kalleta ba yace "waye Ya Muhsin waye Ya Hamad, maisa kowa baya sonki" gabaki daya tabashi labarin gidansu dudda in a childish way ne but he understood everything, sosai take kuka tace "Ya Asad dan Allah kataimakeni kaji, dan Allah karka bari su Abba su koma dani kano dan Allah kataimakeni" tafashe dawani irin kuka mai tsuma rai tana daura kanta akan cinyoyinta, yakai kusan 2min kallon football field din dasuke ciki yake sanan yajuyoda kanshi wani makirin murmushi yasaki for the first time sanan yace "kinason in taimaka miki"? Dawani irin sauri tadago kanta da jajayen idanunta takalleshi dasuke cikemda hawaye, gyadamaikai tayi ahankali tana goge hawayen da bayan idanunta, yana kallonta still yace "are you sure kinaso na taimaka miki"? gyadamai kai tasakeyi cikin muryan kuka tace "eh" tabe baki yayi sanan yadauke kanshi daga kallonta yace "idan kinaso na taimaka miki dole ki koma gida and face ur father and ur Mum" girgixamai kai tayi wani sabon kuka yana zuwanmata tace "wlh zaku komar dani gidan nan dan Allah Ya Asad kayakuri kataimakeni karsu tafi dani" dan juyoda kanshi yayi yakalleta, zubamata mayun idanunshi yayi dayasa taji tahadiye kukan datakeyi tana kallonshi cikin wani irin murya yace "do you trust me"? hakanan taji idanunshi na compelling nata dan batasan lokacin data gyadamai kai ba tace "eh" ahankali yana kallonta yace "I will help you, I have a plan but dole ki koma" gyadamai kai tayi badan tasoba, juyawa yayi yasa hannunshi abayan yazaro wani rag, jefa mata ajiki yayi yace "first thing first clean ur body" dasauri tadauki tsumman ta goge jikinta tass dashi, wani kalan earpod taga yadauko dabatasan na mene ba, gani tayi yayi connecting nashi to wayanshi sanan yajuyo ya kalleta yace "saukar da this thing kasa" yanuna mata gyalen kanta baki, kallonshi tayi ganin yamaida hankalinshi kan wayanshi da abin daya rike a hannu yasa gently takai hannunta taja gyalen abayan kasa, yan kananun kalabanta suka wani bayyana, ga kwantaccen suman gaban goshinta, juyowa yayi ahankali yakalleta, murya chan kasa yace "come closer" matsowa tayi kusadashi ahankali hartanajin saukan numfashin shi kan fuskanta, dauke idanunshi yayi dagakan fuskanta yadaura kan fararen kunnuwanta, ahankali yadauko abin guda daya yakai kunnenta yasamata aciki yana kallon yanda takeda gashi har akunne a kwance, murya chan kasa yace "the other ear" juyoda kanta tayi fuskanta yataba kafadanshi ajiyan zuciya tasauke, gently yasaka mata sanan yakoma sit dinshi yazauna hakan yasa itama yakoma tazauna, ahankali yace "I will help you, namiki alkawari baza'a tafi dake ko'ina ba inhar u do what I will tell u, idan kuma bakiyiba u are on the own, I have one condition koda wasa karki sake kafadama wani ko wata cewa nine na taimakeki understood" yay maganan yana kallonta dasauri ta gyadamai alamun eh, yace "duk ranan da kika fadima wani what happen ranan nida nataimakeki ni din still zansa amaidaki Kanon" dasauri ta girgizamai kai, kunna mota yayi yaja yace "zanuje yanzu, I will drop u outside zaki shiga direct wajensu zaki ki gaidasu, daganan I will be telling you kome zaki fada musu sanan kome sukace zan baki amsan abinda zaki fada musu, remember say exactly what I said kingane" dasauri tasake gyadamai gabanta na mugun faduwa dan gani take kaman wayau yake mata, har gaban gidan sanan yakashe motan yajuya yakalleta yace "gyara gyalen karsu hango abun nan, and don't show them any sign cewa magana ake miki a kunne" sake gyadamai kai yayi, ahankali yace "sauka kitafi" kallon fuskanshi tayi hawaye taji zasu zubomata murya chan kasa tace "Ya Asad dan Allah karka bari su tafidani kano dan Allah kataimaka min" yadade yana kallonta kafin ahankali yace "I will help u Du'a, now go, remember kome nafada miki repeat my words exactly" gyadamai kai tayi tabude kofan tasauka ahankali tabude gate tashiga gida bayan tabar jakanta a motan shi, saida yaga tashiga gida sanan yaja motar shi zuwa gidansu horn yayi aka budemai yay parking awajen parking lot dinsu sanan yay locking motar yana gyara zama ya kara wayanshi saitin bakinshi yanajin sautin karan bude kofan datayi dakuma hayaniya dake tashi afalon. Binta kowa na falon yayi da kallo, ahankali Grandma da ranta ke abace tace "me kikayi anan" hawayen daya zubomata ta share tana gyara tsayuwanta tanajin maganan da Asad yayi sanan takalli Grandma tace "nazo wajen Abba da Mami ne inason magana dasu" kowa kallonta yake, barinma Dad dako kyafta ido ba yayi yana kara kallon halitta irin na ubangiji Baba baki Mama baka, y'a balarabiya, zama tayi ahankali agabansu ahankali tace "Abba ina kwana, Good morning Mami" anatse Babanta yace "Du'a ya kike? Maganan me zakimin bazaki iya bari anjima ba idan mugama magana da kakanki" girgizamai kai tayi ahankali sanan takalleshi tace "Abba Grandma batada lpy sosai, banson sabida ni wani abu yasameta" tsareta da ido Abba yayi sanan ahankali yace "okay to ina jinki menene" shiru tayi kusan 2min takasa magana hakan yasa Abba yace "speak up Du'a, yauzan koma kano" bakinta duk suka gani yafara rawa sosai kaman tana kokarin fighting abinda zata fadi, saikuma ta runtse idanu gam kaman daga sama duk sukaji maganan kaman saukan aradu. "Abba ni aure nakeso!" ba Abba kadaiba da Mami har ita Grandma saida tadan jinkirto daga kujera tana kallon Du'a jin maganan daya futo daga bakinta, tadauki kusan 1min idanunta a runtse sanan tabude idanunta ahankali tadago kanta takalli Abba dake kallonta asanyaye murya chan kasa hawaye na taruwa a fuskanta tace "Abba wlh ni aure nakeso, da inkoma Kano gwara nai aure" tai maganan ahankali dayasa Abba kasa koda motsin kirki hakama Mami dasu Ammi daduk ke falon, ahankali Mami tace "Du'a! Aure kikeso?" Tamata tambayan da mugun mamaki, gyadama Maman nata kai tayi ahankali tace "aure nakeso Mami" Abba da yaji ranshi yasosu sosai da kalamanta yace "Du'a kinsan mekike fadi kuwa? Aure kikeso, wazai aureki? wakikeso to ki aura eh"? Wanan karan shirun datayi yamafi nada sosai lips dinta kerawa takasa fadin maganan dake bakinta hakan yasa Abba da ranshi ke abace yadaka mata tsawa yace "I told you I don't have all day I still have to go back to kano yau, wakike so Du'a!" Yasaka mata tsawa dabatasan lokacin da maganan tafito ba. "Ya Asad!" Tai shiru tana wani irin sauke ijiyan zuciya kaman kirjinta zai fito sanan tace "Ya Asad nakeso Abba!" Wani irin kwalalo idanu Dad yayi, Ammi batasan lokacin dawani irin kayataccen murmushi ya kufce mata a labba ba, surprise look Grandma kemata danyau Du'a takasheta da mamaki, Abba dake kallonta yace "waye Ya Asad" ahankali tanuna Ammi tace "ga Babanshi da Maman shi anan" wanan karan saida Grandma itama tai murmushi bama tagama kai karshen murmushin ba tace "Abba dan Allah ka auramin Ya Asad ina sonshi sosai" wanan karan Abba jiyayi duka karfinshi yakare Du'a humiliated him to the core dabaisan lokacin daya dago kanshi ahankali yakalli Dad ba ahankali Akuma natse yace "waye Asad"? hada idanu Grandma da Ammi sukayi kafin Abba yamayi magana Ammi ta mike zumbur dasauri tace "I think har yanzu baitafi office ba, bari naje gida nakirashi kaganshi Baban Du'a" tafita daga falon dasauri batare data jira amsansu ba Abba da kowa na falon yazubama Du'a idanu. Gida Ammi ta shiga, ganin Ammi yasa Asad yayi kaman irin zai tada motarnan yafita ne dawani irin sauri ta bubbuga kofan motan tace "Asad wait wait" saukar da glass din motar yayi yace "Ammi what is it am late fa office zani" dasauri tace "Asad wait kashe motan kaji I have something very important to tell you, kashe kashe kafito" yanda yaga jikinta narawa yasa ya kashe yafito yana kallonta yace "is everything okay maiya faru Ammi"? Hannunshi takama tarike duka biyun tace "look at me Asad we don't have much time but we will go into deep details later,Asad kasan nina haifeka ko, nai rainon cikinka na haifoka na tarbiyantan dakai zuwa what u are today nataba tambayanka kabiyani ko kasakamin"? dasauri yace "no Ammi" ahankali tace "tom I need u to do something for me, taimako zakayi kuma duk wanda yataimaka ma wani Allah zai taimaka mishi, at this point wata yarinya her life depend on u wlh Asad, please Asad dina, and just know this bazan taba saka kai abu mara kyau ba so u should trust me" kallonta yake kaman wanda bai gane komiba yace "Ammi maizanyi" danshiru tayi kaman wacce ke shakkan fadamai tace "inaso ka auri Du'a jikan Hajiya" dawani irin sauri ya fizge hannunshi yay baya dasauri sauri yace "no way! Ammi, kinsan mekike fadamin kuwa" cikeda damuwa Ammi tabiyoshi hannunshi tasake rikewa tace "Asad bamu da time ana jirana naso dakaine dan girman Allah that's just the only thing I need u kamin right now, any other thing we will discuss it later, at this point kawai u need to save her ne please Asad dan girman Allah idan kana kaunata ni mahaifiyarka, Asad dan darajan Allah karka zubamana kasa a idanu, As......" Ammi! yawani irin kirata da mamaki, cikeda damuwa tace "Asad lemme kneel for u toh halan sainai hakan zakayi" takai gwuiwanta zatasa akasa, dasauri yarike mata hannu yace "Ammi don't kneel for me" kaman zatai kuka tace "Asad I have to kneel for u inhar hakan zaisa kayarda ka taimaken ka auri yarinyar nan nagayama we will discuss d matter later yanzu kawai ina bukatan ka ceci rayuwanta ne inba hakaba tafiya da ita za'ayi, gwara na duka maka Asad na rokeka" tai kaman zatakai gwuiwanta kasa dawani irin sauri yariketa yace "ohhh ohkay Ammi naji basaikin kneeling ba" dasauri ta tashi takalleshi tace "zaka aureta"? Yatsine fuska yayi yace "yes Ammi for now just to save her kuma sabida ke" wani irin ihu Ammi tayi ta rungume shi tana kissing fuskanshi tanamai addu'a kafin taja hannunshi sutafi. Sallama Ammi tayi tabude kofa tashiga Asad biyeda ita kanshi akasa yana cikin suit din aiki, kallo daya Abba yamai yagane yaron dan yaga program din dayayi na youth a channels television news, zama Asad yayi kanshi akasa anatse yace "ina yini Abba" ahankali Abba yace "Alhamdulillah kaine Asad"? Gyadamai kai yayi ahankali yace "tell me about ur self Asad" danshiru Asad yayi sanan ahankali yace "sunana Asad Abdullahi Kitse, I am 33yrs old, nai karatu a UK inada 2 degree my first degree is medicine I am a Doctor, sai na biyun business Administration, currently yanzu bana aiki as a Doctor, business nakeyi inada company kaina" yay shiru daidai nan, gyadamai kai Abba yayi sanan yadaga kai yakalli Grandma dake kallonshi yace "kin yarda da tarbiyan Asad Mama" gyadamai kai tayi tace "a hannuna Asad ya girma nasan waye Asad, na aminta da tarbiyan yaron nan dari bisa dari" gyadakai Abba yayi babu ko alamun wasa tattare dashi yakalli Asad yace "zaka auri y'ata Du'a Asad"? shiru Asad yayi, ahankali Mami tataba Abba, kabarda hannunta yayi batare daya kalleta ba still yana kallon Asad yace "zaka auri y'ata Asad"? kaman Asad bazaice komiba har lokacin kanshi akasa ahankali yace "eh zan aureta Abba" gyadakai Abba yayi yakalli agogon dake daure a hannunshi yaja daya saura, dagakai yayi yakalli Dad dakenan azaune kaman ruwa yacishi yace "bismillah mutashi mutafi masallaci, Asad bismillah" tashi Dad yayi, Asad ma yatashi duksu Grandma na kallonsu suka fita daga gidan, suna zaune nan shiru afalo aka tada sallan azahar akayi sai sukaji sanarwa ana adakata jama'a akwai daurin auren da makocinmu Sanata Abdullahi Kitse yakeson ku shaida, kafin kaceme kawai su Grandma sukaji ana an daura aure tsakanin Asad Abdullahi Kitse da Du'a Muhammad akan sadaki dubu dari. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 4️⃣4️⃣ Ko minti biyu basu karaba sai gasu sun shigo gidan da Sallama, Amsasu Grandma tayi suka shigo, kan Asad akasa kowa yanemi waje yazauna, Abba yadade ahaka sanan yay gyaran murya yace "Du'a" dago kanta tayi ahankali takalleshi, anatse yace "zonan gabana" gyadamai kai tayi ahankali jikinta duk yay sanyi sanan ta rarrafa zuwa gabanshi ta lankwashe kafa, hannunta yakama ahankali yarike yana kallonta yace "Du'a you always feel am unjust towards you, and kinsan wani abu u are right Du'a" Yaydan shiru sanan yace "koma yaya kike u are my daughter and hakkinki ne nakira sunanta cikin yarana so" yadan sakin mata murmushi for the first time tunda yashigo gidan yace "I hope this time around I am just dan namiki abinda kikeso, kince kinason aure kuma amatsayina na mahaifinki na aura miki wanda kikeso wanda Kakarki tayaba da tarbiyanshi bama ita kadai ba ko a masallacin anguwan yanzun nan mutane dayawa sun yaba halin Asad din hakan yakara samin natsuwa hankalina ya kwanta danhaka" yay maganan yana zare hannunshi daya daga rikon dayama hannayenta yatura hannun a aljihu yaciro wrap na sababbin 1k guda daya yadaura akan hannunta yace "ga sadakin kinan Du'a naira dubu dari, Allah ubangiji yamiki albarka" batasan mesa na hakanan taji kuka yazo mata kodan sabida wanan ne karo na farko da Abba kemata magana mai tsayi haka oho amman dai jitayi kuka yazo mata, dagakai Abba yayi yakalli Asad yace "come Son" wani irin murmushi Ammi tayi, ahankali Asad kanshi nakasa yataho gaban Abba shima, hannunshi Abba yakama sanan yadauki na Du'a daya rike yasa asaman nashi yace "ga Y'ata Du'a nan nabaka amananta, ka riketa tsakani da Allah karka cutarmin da ita, ka kulada cinta, shanta, suturanta da lafiyanta dan yanzu duka sun tashi daga kaina ko kan Kakanta sun koma kanka Asad, zuciyata ta aminta dakai dan haka nabar muku ita, yanzun Du'a matarka ce halak malak sai yanda kace sai yanda kace ayi za'ayi dan haka, idan kunso kuyi biki ko taro duk ba matsala takace Allah ubangiji yamuku albarka, zan koma gida zan sanarda Kakanki tachan cewa na aurar dake zan sanarda yan uwanki, kibi mijinki kimai biyayya Du'a, Allah yamuku albarka" yay maganan yana zare hannunshi dagakan nasu yanadan murmushi sanan yakalli Mami da idanunta sukai jajir yace "tashi mukama hanyan tafiya" sanan yatashi yakalli Dad dakawai binsu yakeda ido dankomi yafaru akan idanunshi kaman mafarki ne yabashi hannu yace "surukina sai munyi waya, Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa" dasauri Dad yatashi yana kakalo murmushi yabashi hannu da fara'a yace "Ameen Ameen, zamuyi waya muje namaka rakiya" gyadamai kai Abba yayi yakalli Grandma dake zaune awajen ahankali cikeda girmamawa yace "kiyakuri Mama dakomi, zamu tafi" dan murmushi tamai tace "babu komi baban Hamad agaidamini da yara dan Allah barinma mijina Hamad" murmushi yayi shida Abba suka wuce suka fice, dakin yarage saura Mami data kasa tashi da Ammi dakuma Grandma dake kallonta, tashi Ammi tayi tadaga Mami ta rungumeta bakinta tadaura akan kunnen Mami tace "I know what u are thinking right now Zainab karki manta nima uwace, but zanmiki wanan alkawarin inhar inada rai Du'a bazata taba wulakanta na, zan kulada ita Asad ma zai kulada ita amana, namiki alkawarin nan Du'a tariga tai miji bazan miki karya ba she is in a good hands I assure u that" wani irin ajiyan zuciya Mami tasauke dan har kasan ranta taji dadin kalaman Ammi kankameta tayi tace "thank u Anty Zainab" sakinta Ammi tayi tace "yima mahaifiyarki sallama" gyadamata kai tayi sanan takarasa wajen Grandma ahankali ta tsugunna, dauke kai Grandma tayi hakan yasa gently tace "Mama kiyakuri kiyafemin kinji dan Allah" juyowa tayi takalli yarta ta ga mamakinta saitaga tasakin mata murmushi takai hannunta kan fuskanta tace "komi yawuce, Du'a tayi aure tana kuma kusa dani danhaka komi yawuce, tashi kitafi tafiyan ku nada nisa" tashi tayi ahankali Sana tajuya zata fice hartakai kofa tadan waigo tasaci kallon Du'a hada idanu sukayi hakan yasa tai sauri tafice Ammi dake murmushi tabita abaya dasauri, Du'a batasan lokacin data cire hannunta dake cikin na Asad ba tawani irin tashi cikeda murna tai kan Grandma tafada jikinta tana wuntsula kafa Grandma basu tafi dani ba wayyooo Allah na wlh dadi nakeji yayyy, tawani irin kankame Grandma da mamaki yagama kasheta tana murna, tashi Asad yayi ta gefen ido yakalleta sanan yay hanyar kofa batare daya kalli Grandma ba yace "bari naje office Grandma" baima jira respond dinta ba yafita daga falon wani irin makirin murmushi yasaki tareda biting lips dinshi ahankali yace "killing two birds with one stone feels good, ranshi fess kaman fresh madara.... Saida Abba da Mami suka wuce amotansu sanan Dad yajuya yakalli Ammi yace "what have you done dayasa Asad yace yes to this marriage dan nasan Asad ba son yarinyar nan yakeba, mekikayi Zainab" wani irin murmushi Ammi tayi da zuciyanta daya tace "rokonshi nayi, Alhaji Du'a is a very good girl, ga tarbiya gata so calm, bata bude idanu ba, kuma I am sure ko Asad bayasonta now he will grow to love her trust me and zasuyi making a very nice and healthy family, I just made the best decision for him tr........""Malama kimin shiru" Dad yadaka mata tsawa cikeda fushi yace "what kind of nonsense is all this eh? kinzaci aure abin wasane dazaki lallaba yaronki ya auri yarinyar da batama taba burgeshi ba" ahankali Ammi tace "to inda bai aureta da yanzu sun tafi da yarinyar data kara shiga depression haba Alhaji this girl is so innocent da kallonta kadai zaisa mutum yaji bakison anything that will hurt her, Asad save this girl and muna nan dakai zaisota" cikin kunsan rai Dad yace "just stop with this nonsense idan Asad yashigo gidan nan zan tambayeshi dakaina idan bayasonta this night zansa yarubuta saki yabama yarinyar mutane and free her tunkafin wani abu ya shiga tsakanin su" Cikeda lallashi Ammi takama hannunshi tace "listen Alhaji badanniba dan Allah na yarda idan Asad bayasonta yasaketa but ba da zafi zafi hakaba mutanen nan zasuzo su tafi da ita, adan bari all this heat yalafa tukunna, inhar yasaketa yanzu zasuzo sutafi da ita kano ne that is inma basu maidata kauyen da Mamanshi ke zama ba so please kabar komi ya lafa, dansuma am sure yasami Mamartashi da sauran yan uwanshi kan yama yarinyar aure wani sabon bala'i ne zai barke, amman kaga yanzu da auren nan Asad keda iko da ita kome zasuyi suyi bazasu iya taba tafiya da ita ba kaji" shiru Dad yayi yana kallon Ammi yakuma yarda da maganan ta dan yanzu suna tafiya da yarinyar he stand no chance so dole ya yanke decision din dat is in his interest, kallon Ammin yayi yace "naji bazan sashi yasaketa ba just for now sha sai komi yalafa, my poor boy uwarka tasaka a poor kona" dariya daga Ammi harshi sukayi suna shiga gidansu Ammi tace "he will come around", Dad yace "muje nafadima Turai da kaina nakira Dadda shima nafadamai kafin suji agari" dasauri Ammi tace "wlh amman mubari sai anjima idan ana dinner lokacin kowa na nan, yanzu zokatafi office" gyadamata kai yayi baima shiga cikin gidan ba yashiga mota direban shi yajashi sukatafi Ammi tawuce ciki ranta fess one thing is koma yayane bazata taba bari auren nan ya lalace ba saima tafara tunanin hanyoyin da she will make it work, abubuwan dazaisa danta yaso Du'a sosai. Gidansu yashigo ranshi fess yaja motanshi yatafi office abinshi. Saida Asad yafita Grandma taji karan bude gate da fitanshi sanan ta daddage ta dakama Du'a dakekan jikinta duka acinya tace "tashi dan gidanku kidubeni nan" tashi zaune tayi ahankali tana turobaki, Grandma tace "ba asama na barki ba da yaushe kika fita danaga kin shigo ta kofa" turo baki tayi tace "ta window" shiru Grandma tayi tana kallonta anyway bama ta tambayan nan takeba wanan ne most important one ahankali tace "Du'a yaushe kika fara son Asad" sosai take kallon Grandma lips dinta harrawa yake tanaso tafadi mata gaskiya but tana tuna uban kashaidin da Asad yamata, tashi tayi takai hannayenta kan fuskanta tace "ni kunya nakeji" tai stairs da sauri tanadan dingishi, tafi Grandma tayi tace "jama'a yau naga yarinya, agaban kowa tagama cewa tanason yaro, yanzu ni dana tasata agaba ina mata tambayan shine take cemin tanajin kunya ai shikenan" tai maganan tana murmushi wlh bazatai karyaba har cikin ranta taji dadi, tun ranan da Hamad yakawo Du'a data daura idanunta akanta aranta taji zataso tahada Asad da Du'a aure, sai gashi Allah yatayata kome zai faru yafaru she will make sure that this marriage work, kwalama Razika da Shemau kira tayi dasauri suka fito, cikeda fara'a Grandma tace "kuzo inaso na aikeku kasuwa direbana na kaiku ku sayomin sweet da goro, an daurama Du'a aure da Asad dan wajen Ammi yanzun nan mahaifinta a masallaci kutayani murna" gani kawai Grandma tayi sunhau tsalle, Razika tace "Ammi ni duk idan yazo gidan nan dama nakanji inama ace Du'a budurwanshi ne wlh naji dadi" dariya Grandma tayi tace "nima haka, ungo kudin nan kuga kuje ku sayomin narabama jama'an Annabi suci su shaida su sama auren jikata albarka insha Allah mutu karaba, wuce kutafi" karban kudin sukayi, Grandma tadau wayanta takira danta tasanar dashi sanan tashiga kiraye kiraye tana sanarda jama'a. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 4️⃣5️⃣ Wuraren Magrib suka shigo gidan, motan Sharif ne agaba na Asad biyedashi, suna parking suka fito agurguje sukai alwala anan pampon tsakar gida sanan suka fita zuwa masallaci salla sukayi suna idarwa Sharif yaga sai musabaha akeyi da Asad ana cemai Allah ya sanya alheri Allah ya sanya albarka, tabe baki yayi yace wanan hala yasayama masallacin wani abune, gaba yayi dan yunwa yakeji, Asad din yabiyoshi daga baya, suka shiga gida Sharif yace "muje muci abinci please I am starving" hararan Sharif din yayi hakan Yasa Sharif yaja hannunshi yace "common d more kana gudunma Anty Turai d more tanamaka iskanci idan ta ganka muje jor" janshi falon yayi kowama zaune a dinning harda Dad ganinsu yasa Dad yace "daman ku muke jira let's eat" karasowa sukayi ahankali yace "evening everyone" sanan yaja kujera yazauna Anty Turai ta ballamai harara amman ko kallonta baiyiba, ahankali sukecin abincin jikake tsit babu mai magana ma Aneesa sai satan kallon Asad din take dataga yamata kyau, saida aka gamacin abincin sanan Dad yadau tissue yashare bakinshi yace "nobody should leave the table akwai abinda zan gayamuku listen up" duk gyara zama sukayi suna kallon Dad din banda Asad da yaciro wayanshi yana daddannawa, gyaran murya Dad yayi yace "I believe dukan ku nan kunsan Du'a, Du'a yarinya ce that has been through a whole lot.........nan yabasu labarin Du'a har zuwa dalilin zuwan ta Abuja everyone was shock barinma Sharif dayaga he's a bit closer to him and bata taba gayamai rayuwanta ba, sanan Dad yacigaba yace "yau mahaifinta da mahaifiyarta sunzo........ nan yabasu labarin komi harzuwa inda Du'a tace Asad takeso har aka daura aure har kawowa yanzu" yanda gaban Sharif ke fadi haka na Aneesa kefadi danasu Rahima dan sunsan yanda Sharif keson Du'a, haka kuma sunsan yanda Aneesa keson Asad dudda bata taba fadamusu da bakinta ba, kasa hakura Sharif yayi yajuya yakalli Asad dake daddanna waya abinshi kamanma baisan mesukeyi ba yace "kai kanason ta ne Asad" girgixa mai kai yayi yana tabe baki, cikin yanayin wulakancin nan da halin basarwa irin nashi yace "Ammi made me do it" dukansu juyawa sukayi suna kallon Ammi, dasauri Ammi tabude baki zatai magana Dad yace "yes Ammi ku tasa yay haka but I am in support of hakan datayi inba hakaba tafiya da ita zasuyi maybe ma amaidata kauye, so for now abar maganan aurensu ahaka harzuwa komi yay sanyi ya lafa, auren is not like irin eh aure aure is just to save the girl ass, dazaran komi yalafa Asad zai iya rubuta mata takarda and free the girl idan tasami miji ta auri duk wanda takeso" ahankali da Anty Turai ranta yake a mugun bace tadan saci kallon yarta dake gabda kuka amman daurewa kawai take jitayi ta harzuka sosai tace "maganan banza maganan wopi, wani irin banzan abu kukasa danku yayi eh? Ina ruwanku dawata Du'a ba dangin iya bare na Kaka haduwan Abuja, yar uwanmu ce ko danginmu ne dazakusa yaro ya aureta just to save her, ba kauyeba ko wuta sukakai yarinyar me ruwan mu ba yarsu bace inma sun kasheta ai su suka haifi kayansu, ni dama tun ranan dana fara ganin yarinyar naji bana sonta, nidai wlh inhar da raina banyi accepting auren nan ba so I as much am concern Asad is still very single in my eyes kuma zamu nemamai mata......" tsareta Dad yayi yace "to menene abin tada jijiyoyin wuya anan Turai eh? Kedai wlh baki raina abin fada, shi yaron kinga yanaso ne"? Cikin fushi tace "wani irin tambaya Yaya kakemin haka? Asad fa namiji ne eh? Inhar yarinya nada nono da duwawu mezai hana kar Asad yasota nan gaba? Anfa riga an daura aure yarinya tazama tashi halak malak, namiji anbashi mumnunan yarinya dabayaso amatsayin mata yadurama yarinya ciki balle kuma anbama Asad mai kama da mayun nan dako yan uwan ta tsoronta suke, ai wlh Asad ya shiga kenan, ni wlh ku masifan batamin rai and nagayamuku I will never ever accept that girl, Yaya sabida rashin mutunci da rashin ganin amfani na ma ace ina gidan nan fa babu inda naje, ni kadaice kanwarka yar uwarka aduniyan nan amman kuje kuyi abu dagakai sai munafukar matarka baku sanar dani ba san......" Tashi Sharif yayi fuuuu yawuce yafita, Turai tabishi da kallo, ahankali Asad dake daddanna wayanshi yatashi yabishi yafice shima, tashi Aneesa tai dagudu tai sama su Rahima da Mariya suka bita sama itakuma Anty Turai tashiga surfafama Dad da Ammi bala'in ta inda take shiga batanan take fitaba Abba yay shiru kaman ruwa yacinyeshi dan he's even confused, ba'a taba trusting namiji da mace shi karan kanshi bazai iya kirga mata munana da bayasonsu yan office dinsu dayaci ba, baya sonsu ko kadan amman saida yacisu balle kuma mai kyau, what if Asad sleep with this girl, what if yama yarinyar nan ciki ga yarinyar da shegen kyau ya zaiyi kenan?..... Fadawa kan gado Aneesa tayi tafashe dawani irin mugun kuka, shigowa su Rahima sukayi suna maida kofan suka rufe, ahankali Rahima takaraso gaban gadon ta zauna tana shafa kan Aneesah tashi tayi dagudu ta rungume Rahima sosai tana wani irin kuka, ahankali Rahima tace "kiyakuri Aneesah ba" dasauri Mariya tace "kiyakuri Aneesah ni banmaga abin kuka ba kema ai kinsan Asad bayasonta kumama ai temporary aure ne" wani irin hararanta Rahima tayi tace "angayamiji akwai wani abu waishi temporary aure ne aduniyan nan, ni wlh Sharif ma yafi bani tausayi, ita Aneesah babu wanda yasan kina naki ai komu baki fadamana ba, shiko Sharif ya nunama kowa yanason Du'a, kwata kwata Ammi batai planning abin da kyau ba but nasan harda sabida Asad ne agida Sharif bayanan da am sure Ammi Sharif zatasa ya aureta dan yafi kirki dan Ya Asad dakeda bakin halin nan ai gana mata azaba zaiyi" dagakai Aneesah tayi cikin kuka sosai tace "da yardan Allah sai Ya Asad yagana mata azaban da saitai dana sanin cewa tana sonshi, wlh wlh Du'a mayaudariya ce kuma makira ce algunguma maicin amanan friendship, ita kadai nafadama inason Ya Asad" dasauri su Rahima har suna hada baki sukace "dagaske" gyadamusu kai tayi tace "ana gobe birthday dina ranan Thursday wlh saida na gayamata har tana cemin tona gayamishi ai gashi ita tagayamai, wlh Du'a makirace Allah ya isa tsakanina da ita wlh bazan taba yafemata ba duniya walahira wlh wlh ko" tsabagen bakin ciki tama kasa magana sai kuka, ta bala'in bama su Rahima tausayi. Ahankali yatura kofa yashiga dakinsu tsaye yaga Sharif yakafa goran ruwan sanyi abaki yanasha kaman wanda yaje yaki, dan tabe baki yayi yawuce stairs abinshi, binshida kallo Sharif yayi kawai yacire goran ruwan daga bakinshi ya jefar ruwan yazuba atsakar dakinsu wani irin kifa kanshi yayi a fridge din yana kokarin daidaita heartbeat dinshi yace "Ammi why? Why? Eh" ahankali yazauna a kasan bango yakifa kanshi yana magana shi kadai ahankali. "nasan ni kika fara nema rashin ganina yasa kikai reaching out to Asad for the help, Ammi maisa baki kirani awaya ba? Don't u know that Asad is bad choice ma Du'a haaa? He will maltreat the poor gurl and make her suffer, Asad baya sonta" wani hawaye mai zafi ne suka zubomai dasauri yashare ahankali yace "but Dad yace ita dakanta tace tanason Asad, Du'a how could u love Asad mutumin da all abinda zaiyi shine ya wulakanta ki and make u cry all the time" ajiyan zuciya yasauke yace "I've been so good to you starting from the first day dana fara ganinki aduniya, ta dalilina kike araye yau, I forced Asad to save u a rijiya, I've been very generous good and romantic towards u but all this baki ganiba kikaje kinason wanda bai damu dakeba daidai da zarra daya, maisa mata sunfison mazan that makes them cry always mazan dake wahalar dasu eh"? Wani irin fashewa da kuka yayi mara sauti awajen yana taushe bakinshi he is deeply hurt, like deeply, part din da Du'a ne tai proposing komi shiyafi cimai zuciya, ko kadan baya ganin laifin Asad dan yasan tursasashi akayi. Asanyaye Asad yamaida kofan dakinshi yarufe tareda jingina da kofan yana lumshe ido dan he could hear sautin kukan Sharif dan dakin komi akashe yake ba'a kunna AC ko TV so so zakaji sound na komi very well, ahankali yazauna akasa gaban kofan still idanunshi a lumshe, he really care about his brother yanason Sharif sosai he hates seeing him hurt, ahankali yace "I am so sorry Sharif, I am sorry". 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR EPISODE 4️⃣6️⃣ Wani irin lafiyayyen bacci tayi da kyar ta tashi shima sabida Grandma data tadata ne tawuce tafice ahankali ta tashi zaune da kyar tana hamma, sanan tasauko da kafafunta tamike tsaye daga gado jin tsamin da kafafun nata sukayi jiya duksun bace yasa taji wani dadi tawuce ta tafi bayi, brush tashigayi saikuma tadago kanta ahankali ta kalli kanta ta cikin madubi tace "ke matan aure ne yanzu fa Du'a" wani irin kawarda maganan tayida sauri dan daga ita sai Asad sukasan komi tasan wanan ba aure bane besides ma ita ai taroki Ya Asad to save her gashi kuma hakan dayayi really saved her dan bagashi Abba da Mamin ta duk sunzo sunkoma ba'a tafida ita ba, so all this ba aure bane, ina zamata iya auran Ya Asad dinan mugu, zata sami mijinta mai kirki kaman irinsu Ya Hamad dasu Ya Sharif suyi aure abinsu, karasa brush din tayi tana wani irin murmushi dan harga Allah murna sosai take ta tsani kano sosai rashin tafiya da ita ba karamin dadi yamata bata ganin anything sama da hakan, alwala tadauro sanan tafito tai salla tana idarwa ta zauna tana biya karatun da malaminta yamata sanan tazo tai assignment din daya bata duka tamaida books din jaka sanan ta tashi, fitowa tayi tana tafiya ahankali tasauka kasa dan yunwa takeji sosai, Grandma tagani zaune a falo tanajan charbi ganinta yasa dasauri ta tsinke charbin datakeja tace "ke yau zakije aiki ankawo komi naki jiya kinyi bacci, wuce kije kiyi wanka kiga" turo baki tayi dan bataso tajeba takoma sama, wanka tashiga, koda tafito saitaga anfito mata da kayan dazata saka, wani baki da golden abaya ne mai mahaukacin kyau tagani akan gadonta, dasauri tai wajen abayan tana dagawa tace "wow yaushe Grandma tasaimin wanan" ijiye rigan tayi sanan takoma gaban mirror tadauki mai ta shafa sanan ta fesa bodyspray sanan tadauki rigan ta shirya tsaf cikinshi tana kallon kalaban kanta da duk suka soma warwarewa da kansu dan haka gashinta yake yatsine fuska tayi tadauki ribbon takullesu sanan tawuce tafito kasa zuwa dinning zama tayi Razika tafito daga dakinsu tana mata murmushi tace "mezan zuba miki?" Irish tafadi tana kallon soyayyan Irish din, zuba mata Razika tayi sanan tamiko maka karba Du'a tayi tace "thanks" sanan tadau fork tafaraci, dagakai Razika tayi takalli Grandma ganin lazimi take abinta yasa Razika tazagayo taja kujeran kusada Du'a tazauna tana kallonta tana murmushi tace "sannu Amarya ke kodan kunyan nan da kawaici na amare bakiyi" kallonta Du'a tayi kaman wacce batagane me ake fadiba tace "wacece amarya"? hararanta Razika tayi tace "kece mana jiya duk munje mun gama raba cingum da sweet, Allah Du'a namiki murna sosai Asad dinan yahadu wlh gashi baya wasa da mutane baya murmushi, u are very lucky dakika aureshi" kallonta Du'a take da ace tasan wanan ba aure bane daduk batai maganganu hakaba, gyadakai kawai tayi tadauki cokali tacigaba da cin Irish dinta sanan tadau tea kurba daya tayi kawai ta tashi zata wuce Dasauri Razika tace "wai har kinci abinci kenan Du'a "? gyadamata kai Du'a tayi alamun eh, dasauri Razika tace "Irish din dakikaci banjin su kai guda 10 bafa wai mesa bakison abinci ne Ulcer sai kamaki fa" cunno mata baki Du'a tayi tawani juya tai sama Razika tabude baki ganin wani tsiwa ma takeji da safen nan, shafa lazimin da Grandma takeyi tayi takalli Razika tace "ai Du'a sai dai Allah yatarota karki biye mata sami kula mai kyau ki zuba mata abinci tatafi office din dashi danni ban yarda Ulcer yakamata ba ba gaira ba dalili atoh" murmushi Razika tayi taje kitchen tadauko wani karamin kula mai kyau ta zubamata chips din da plantain tasan yanda takeson nama hakan yasa tazuba mata soyayyen naman kasa ciki, daidai nan tasauko tana duba jakanta taga kotasaka komi Tao rolling gyale dudda babu komi akan fuskanta amman tai bala'in kyau, ganinta yasa Grandma tabita da kallo murmushi tayi tace "kawo kulan nan kiga Razika" karasowa tayi rikeda kulan tana kallon Du'a data tsaya atsakiyan falo tana kallonsu, karba Grandma tayi tamikama Du'a hannu tace "bani jakan nan" turobaki tayi tace "akwai wajen cin abinci fa a office so kike acemin yarinya zan wani tafi da abinci" hararanta Grandma tayi tanasa kulan ajaka tace "dabakison kijeda abincin da kinci da kyau, zo ga national ID card dinki yafito gakuma account number ki nan rubuce akan paper nan ga ATM card dinki" zama tayi kusada Grandma tana duba komi tana murmushi sanan takalli ATM CARD din daga sunanta ajiki tai wani irin murmushi tace "nima yanzu inada katin cire kudi" tabe baki Grandma tayi tana kallon agogo takwas saura tace "wlh Du'a kikai latti mijinki Asad daidai yake dake" dasauri takalli Grandma jinta kirashi da mijinta wani bambaran abin yamata tashi tayi tana zuba komi ajaka sanan tarataya jakan tace "natafi Grandma, Razika bye" tama Razika dake kallonta waving hannu dan Du'a tamata mugun kyau kodan andaura mata aure jiya ne oho amman yau taiwani irin special kyau kaman wata Amarya. Motan Grandma tashiga bayan tagaida direban dake tsaye gaban mota, shiga yayi yajasu bini bini yana kallonta ta glass din motar dan arayuwa baya gajiya da kallo jikan Hajiya nan mai kama da balarabiya, shigowa kampanin sukayi yay parking a parking space ya kashe motan fitowa daga motan tayi ahankali sanan tasa hannu tadauki jakanta dakekan kujera sanan takalleshi tace "thank you Uncle" sanan tamaida kofan tarufe tajuya tana tafiya ahankali tana kalle kalle, sanan takai gaban entrance tashiga, tana shiga receptionist din wajen dake kokarin kwasan wasu files jikinta narawa takalli Du'a tace "why are u late Miss Du'a? Anyway there's no time for that kiyi sauri sauri kije hall a 2nd floor, Mr Asad is having a meeting with all staff duk ana wajen hurry" yanda tai maganan jikinta narawa tana parking wasu files yasa dasauri itama Du'a tajuya tai bene Receptionist din tabita da kallo, second floor din takai babuko kowa awajen alamun duk ana meeting ganin wani babban kofa guda biyu haka da aka rubuta hall ajiki yasa tai wajen, ahankali ta tura kofan ganin ko gezau baiyiba yasa tasa duka karfinta tawani irin tura kofan kofan yawani irin budu doors din sukai slamp din bango jikake bam ba dayasa kowa naciki yajuyo yana kallon kofan harda Asad dake magana agaba tashiga ciki tana sauke ijiyan zuciya, Babban Hall ne sosai kaman irin na school dinan kowa na wajen harda security, na gate kawaine basa wajen, ga Asad dake sanye dawani dark blue suit yay azababben kyau ya gyara gashin shi tsaye agaban hall din gaban wani speaker haka dake kan mumbarin yana bada speach sai Sharif dake sanye da suit mai ruwan toka zaune kan wani hadadden chair agaban hall dinma da MacBook akan table dinshi da byro alamun ana aiki ne shima, shigowanta da yanda ta bude kofan yasa yadago yana kallonta, wani kalan rawa jikinta yayi hakan yasa bakinta nadan rawa sosai tabude baki cikin yar zazzakan muryanta tace "Sor.....ry" tai maganan tana saukarda kanta kasa first kujeran dake right side dinta taja tazauna hakan yasa kowa yamaida kanshi yajuya, ahankali Asad yadaga hannunshi fuskanshi babu alamun wasa ko kadan, agogon hannunshi yakalla tara saura kwata hakan yasa yasauke hannunshi bakinshi na saitin speaker yace "Miss Du'a" dawani irin sauri Du'a tadago kanta jin sunanta a speaker da hall din ya amsa tashi tayi dasauri kirjinta na dukan uku uku takalli Asad din dake kallonta fuskarnan ba rahama yace "u are late and in my meeting I don't welcome late comers, excuse us" yay maganan strictly, gyadamai kai tayi tasan menene excuse but batagane kalan excuse din dayake nufi ba anan, ahankali takoma tazauna tana tunani kaman daga sama taji tsawanshi. "I said leave this hall or are u deaf" wani irin firgita tayi batasan lokacin data zabura taja jakanta jikinta na rawaba kanta akasa sabida yanda ake kallon ko kadan bata lurada receptionist data shigo da lots of files da Asad requested for ba, wani irin karo taji taci da mutum tai baya kan kaceme receptionist da dama files din sun mata yawa a hannu hill din kafanta ya turgude tayo gaba kafin tafado files din suka fara zubowa kan Du'a da already tazube akasa, ihunta ma kasa fitowa yayi sabida files din dake kan fuskanta saiga receptionist da itama tafado kanta, dawani irin sauri receptionist din ta tashi jikinta narawa tace "oh my God, oh my God I am so sorry" tai maganan tana kwashe files din dake kan jikin Du'a, ahankali tadaga hannunta tasa hannun ta ture files din idanunta har sunyi ja ga hawaye, ijiye files din reception din tayi takai hannunta kan fuskar Du'a tace "oh my God I am so sorry, are u hurt? Stop crying" ahankali Du'a ta lallaba ta tashi tana share fuskanta da duk kiran files din kekai, sanan tawuce tafita batare data juyoba, 5th floor dinsu tawuce taje bathroom dinsu wanke fuskanta tayi tass sanan ta wanke hannunta ta kakkabe jikinta tana turo baki, kaman tawuce ta tafi gida amman tunawa da maganan Grandma da inyacee get out bawai koranki yayi ba kuma karta sake irin abu da tayi last time yasa ahankali tabude kofan bayin tafito sanan tawuce office dinta, ahankali tabude office din tashiga zama tayi ahankali tana kuyi akan kujeranta saikuma tai murmushi tanason dan office dinan, wayanta taciro tana kallo rabonda tashiga watsapp kotama kunna data harta manta tun kafin birthday din Aneesa dan ita wayan da chatting dinma bawai ya dadata da kasa bane dan bamata sababa daman Grandma ce ma ke kiranta wani zubin yan gidansu babu mai kiranta ko Mami bata kiranta saikuma su Aneesah wanda su yawanci chatting ne, ahankali ta kunna data, ajiye wayan tayi tadauki kukan da Razika tasamata abinci budewa tayi ganin nama asama zako zako yasa tai wani irin murmushi tadau guda daya takai baki sanan tadau wayanta da dayan hannun ta shiga watsapp ganin messages dinta na shigowa, tana shiga taga messages din duka daga groups dinsu na yammata ne wanda su Aneesah suka sata, daman shi kadaine group din datake ciki, dasaurinta ta danna ta shiga group din the first abu datagani shine Aneesah removed you, dan zaro ido tayi tace mistake ne, sanan idanunta suka sauka kan message din Mariya tasa announcement group Du'a is no longer our friend in fact she's even an enemy, dan dariya Du'a tayi dan she always known Mariya to be a bit wild and Crazy, Rahima da Aneesah sunfi sweet da kirki da iyamagana, tacigaba da karanta messages din tanacin namanta, wata daga cikin kawayen su tace "Du'a Du'a wanan kyakkyawan yarinyar damuka gani a birthday dinku dako kallonmu batayiba, metayi muku?" taga yan group din nata fitowa suna tambayan meta musu, Mariya ce tasake fitowa tai reply da "she's a snitch, a hypocrite, and very cruel, kunsan yanda mukeson yarinyar nan kuwa? We share all our things da ita, har saka yayyanmu muke yabata kudi muje shopping da ita shine zataci amanan mu" wanan karan dan fadi gaban Du'a yayi dan she understood this is not more a joke, yan group din sai tambaya suke metayi metayi, saiga Aneesah tafito tace "she stole my boyfriend tama aureshi dazu aka daura musu aure, bayan tasan ina sonshi he mean the world to me this girl knows everything about me shine zataje tabi tabayana ta yaudaran, wlh wlh bazan taba yafemata ba duniya walahira, Allah saiya sakamin yar iskan yarinya Aljanna kawai mayya, barima nabaku labari daga ubanta har uwarta duka nadaman haihuwanta suke basa sonta anma kawota nan Abuja wajen kaman just to save her ass ne, yarinyar that has been bad luck and wahala to her parents uban waye bazata tababama, shegiya mai bakin jini, asararra aljanna kawai" dawani irin gudu tafito daga group din takasa karanta sauran messages din kuka tafara ahankali zaginda Mariya tamata baima bata haushiba na Aneesah ne yamata ciwo harda kawo maganan gidansu, ahankali tasake daukan wayan tana share hawayen da hannun riganta ganin not just group tanada individual messages from different numbers da duk batadasu yasa ahankali tabude na first one wanda shi dasafen nan yashigo. "This is Vee Aneesah's friend, you this bastard girl how dare you kikamata snatching boyfriend eh, wayeke ke yar gidan waye keda ubanki of all people HOD ne, kinsan waye uban Aneesah kinga gidan masu kudi shine kike neman space, bakisan ba'a ma yammatan Nile snatching boyfriend ba, wlh wlh kin shiga uku watch out for your self, mayya kawai mai kamada aljanu duk maitanki kanki kawai zaki iyaci munfi karfinki munbaki 2days kirabu da Asad inba hakaba wlh saimun kasheki" wanan karan sakin wayanta tai akan table ta tashi dagakan kujeran takoma gefe tana kuka ahankali, bude kofanta da akayi yasa tadago kanta dasauri, hada ido tayi da Asad dake kallonta dawani irin sauri tasa bayan hannunta tana share fuskanta lips dinta har rawa suke tace "good morning Sir" dauke idanunshi yayi daga kanta yabi office din da kallo kafin idanunshi yasauka kan table dinta da jaka kekai ga kula abude na abinci, ga naman da aka faraci akan table ga wayanta da screen din ke haske sosai karan messages na shigowa nata shigowa wayan, ganin ya tsare wayanta da kallo yasa dagudu tai table din tasa hannu ta dauki wayan taboye abayanta tanajan hanci trying to stop the kuka kanta akasa. Hannu yamika mata murya chan kasa yace "give me the phone" girgixa mishi kai tayi ahankali tace "is mine" danta dauka yadauka wayan office dinsu ne, cikin harsh tone yace "I said give me the phone" dago kanta tayi ta kalleshi ganin idanunshi da babu wasa aciki yasa kaman am tsinke mata wani abu ajiki ta zagayo duk yana binta da kallo tazo gabanshi ahankali ta tsaya sanan taciro wayan daga bayanta ta mikamai, karban wayan yayi yana batarai yace "clear this table sort yourself out and meet me in my office in the next 10min" sanan yajuya yafita daga office din. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 4️⃣7️⃣ Zama yayi akujeran office dinshi yana kallon wayanta da har yanzu messages me shigowa, bude wayan yayi ganin babu pin ko password yasa ya shiga ciki, watsapp dayake ta ganin messages na shigowa ya shiga yana kallo yawancin messages din dake shigowa now ma batada contact din, first message din ya danna ya shiga. "kirabu da Asad inba hakaba no peace for you, kedin uban waye ke dahar kin isa ki kwacema Aneesah boyfriend, mun baki 2days" dan jim yayi dan to be honest bai gane me ake cewa ba, hakan yasa yazauna yabi messages din duka ya karanta harda na wanda zasu karanta dakuma group din friends forever dayaga ancireta yabi chats din yakaranta jiyayi ranshi ya bala'in baci su Aneesah da Mariya da kawayensu ke zagin Du'a haka, fitowa yayi daga group din yabi messages dinta tass nada yaga bata chatting da kowa banda su Aneesah dama fitowa yayi yashiga normal message dinta daga message din data saina MTN, contact dinta Grandma driver sai nasu Aneesha sai kuma contact din dayaga ansa Yayana, danna contact din yayi yaga number Sharif ne, gallery yabude yashiga babu komi ciki sai hotunan ta datayi yawanci tana kan gado ne da kayan bacci ajikinta dakuma wanda take kwance ajikin Grandma da shimi ajikinta tana turo baki idanunta sunyi kulu kula alamun Grandma tazo tadata ne, wallet dinshi yaciro yaciro wani pin ya ijiye gefe sanan yashiga watsapp din nata yay deleting account din daga watsapp gabaki daya sanan yadau pin din yazakulo wajen simcard, MTN Sim din yacire sanan yakashe wayan yaja locker dinshi yasa wayan aciki kafin yadau Sim din ya kakkarya yabude wani fine dutsin irin na yangayun nan dake gefenshi yajefa line din aciki daidai lokacin anyi knocking ta laptop din gabanshi yaduba ganin itane gaban kofan yasa yace "come in" shigowa tayi kanta akasa ta share fuskanta tass, tunda tashigo yake binta da kallo harta karaso gaban kujeran, kaman ance dole yay maganan yace "sit" zama tayi kan kujeran tana sauke ijiyan zuciya dashi kanshi saida yaji, laptop yaja gabanshi yafara aiki yace "ur card and bank details" jakan data shigo dashi tabude taciro komi sanan ahankali tadago kanta tamikamai hankalinshi nakan system din dayake aiki akai yabata hannunshi, samai ahankali tayi ciki sanan tamaida kanta kasa, saida yakarasa abinda yakeyi sanan yadago kanshi yana kallon National ID CARD din nata, sanan yaduba takardan da aka rubuta mata account number yaga First Bank aka budemata, ijiye duka biyun yayi gefenshi dan zai bada ayi scanning asaka a file dinta, maida kanshi yayi jikin system din yacigaba da aikin dayake, murya chan kasa kaman wanda baiso yay magana yace "this is ur second late coming, idan kikai 3rd one u are leaving my company dan late coming is completely not allowed in this organization, go to you office I've sent u list of what u gonna be drawing yana printer dinki" gyadamai kai tayi ahankali tadago kanta takalleshi kaman tacemai yaushe to zasu rabu yasaketa tunda ai daman auren he did it dan yataimaketa kar a tafi da itane kuma gashi ba'a tafi da itaba basai ya saketa ba sabida Aneesah tagani there's nothing like yaudaranta datayi, yama za'ayi tayaudari Aneesah her friend. Dago kanshi yayi suka hada ido ganin yanda take kallonshi, harwani irin firgita tayi dawani irin sauri ta mike dagakan kujeran zumbur tawuce tafita harda dan gudun ta. Tana bude kofa saura kadan taci karo da Sharif dake kokarin shigowa office din ganinshi, dasauri ya matsa gefe karta fado ajikinshi da bata tafa bango ba da babu abinda zai hanata faduwa amman batadamuba wani irin dadi taji aranta ganinshi dan rabonda taganshi tun ranan birthday Aneesa cikeda fara'a tace "Ya Sharif good morning" dauke idanunshi yayi daga kanta yabude yakara tura kofan da already ke abude dama yashige office din batare daya kulata ba, dasauri tabishida kallo surprisingly har zuwa cikin office din, hada ido datayi da Asad yasada wani irin sauri tawuce tashiga office dinta tana mamakin yanda Sharif yashareta saikuma tace hala baiji nakirashi bane, saikuma tai shiru tace but ko baiji ba ai Ya Sharif kullum yaganni saiya kulani, saikuma tace ko sabida mugun nanne Ya Asad halan shima yana tsoran fadanshi saisa bai kulani ba, da haka tai concluding takarasa gaban printer tadau paper datagani ya bullo tana dubawa ware idanunta tayi tazaro su waje, tace "tayaya zan iya zana 100 designs na flat shoes da 150 designs na hills? How? soyake idea kaina ya kare tass, tayaya zan zana" tai maganan tana wucewa tazauna tace "kuma I have to submit it today ai there's no enough time ma, wanan ai mugunta ne" tai maganan tanaji kaman ta fashe da kuka, ganin tana kara wasting time ga lokaci na tafiya dan yanzu sha biyu saura yasa ahankali tamika hannunta tadauki drawing board din sanan takara dauko wani guda biyu, tashi tayi tadauki komi sanan tadawo tazauna, hannun riganta ta tattare ta gyara zama tafara zanen looking damn charming, indai tayi kadan saitaci namanta dasu Irish, zanen ma saiyasa ta manta dasu zage zagen gabaki dayan hankalin ta nakan zanen, saida taji kiran salla sanan ta tashi tabude kofa tafito tana kalle kalle tana mamaki maisa Ya Sharif baizo yakirata ba, sauka tayi tai alwala tashiga masallacin tai salla sanan ta tashi tafito, ganin Sharif yafito daga masallacin yasa dasauri takarasa saka takalmin nata ta kirashi dasauri Ya Sharif, amman kojuyowa baiyiba dawani irin gudu tabishi, lift yashiga bata damuba tafada tashige ko kallonta baiyiba yadanna 4th floor, agabanshi ta tsaya tana kallon fuskanshi cikeda damuwa tace "Ya Sharif menene bakada lafiya ne? Inata kiranka baka amsani baka biyomin munje masallaci ba" fara aikin da lift din yayi yasa ta tsugunna da sauri kaman zata fadi dasauri yakalleta, dan dago kanta tayi takalleshi cikinta namata wani iri tace "menene wai anbata maka raine tun safe u didn't say a word to me" tsayawa lift din yayi daidai ankai 4th floor din kofan yabudu Asad suka gani tsaye gaban lift din wani worker na nunamai abu awani file ga dukkan alamu elevator yake jira, ganin Du'a tsugunne kusada Sharif dake tsaye looking straight yasa yadauke kanshi kaman baigansu ba yana sauraran maganan da mutumin yakemai, fitadaga elevator Sharif yayi dasauri Du'a ta tashi itama zata bishi tana zuwa wajen Asad batare daya kalleta ba koyacire idanu daga abinda mutumin ke nunamai ba yasa mata kafa jikake tifff tai wani irin wawan faduwa tai kara da saida yasa Sharif dake shirin shiga office yajuyo dasauri daidai lokacin Asad na maida kanshi back shikuma employee dake dakema Asad magana yazo inda Du'a take dasauri yace "OH my God miss are you destined to be falling like this ne yau, tun safe kike faduwa sorry tashi" batare da Asad yakallesu ba yawuce yashiga elevator yace "give her the files takawomin" dasauri employee yace "yes sir" yamikama Du'a dake tashi tsaye da kyar tana tana guiwanta file din, dauke kai Sharif yayi ahankali yabude kofa yashiga, juyawa Du'a tayi ganin yashiga office dinshi yasa tajuya ahankali takalli Asad dake tsaye cikin lift yaciro wayanshi yana dannawa, dasauri employee yace "hurry Oga is waiting" wucewa tayi tashiga elevator tana tafiya ahankali ta tsaya jikin bango, maida wayanshi Asad yayi aljihun jacket dinshi sanan yasa hannu ya danna grandfloor, kofan lift din yarufe dasauri ta tsugunna kasa ahankali tana shirin lumshe ido ganin yafara tafiya taji anwani irin finciko azabure tabude idanu, Asad ne yawani jata kaman tsumma dan saida yama cire rolling din datayi duka tsabagen yanda ya fizgeta, wani irin makalata yayi jikin bangon elevator din yasa duka hannunshi biyu yashako wuyanta idanunshi sunyi wani irin mahaukacin ja jijiyan gaban goshinshi yafito sosai abinda bata taba ganiba, wani irin nishi take jin yanda ya shaketa tanajin hucin hancinshi akan fuskanta, daidai nan elevator yakai grand floor da kafanshi ya danna wani botur daya datse kofan ta yanda duk wanda zaizo bazai budeba, sanan yajuyo yakalleta, wani irin juyawa idanunta suka fara tana firfir da hannu kaman zata mutu, cikin wani irin murya dabata fita sosai tsabagen yanda ranshi ke zafi yace "duk randa naga kina bin wani namiji ko kina kula wani namiji wlh saina kasheki, this should be the first and last time dazanga kinyi magana da any namiji ko anan koma a ina, understood" yadaka mata wani irin tsawa jijiyan kanshi dama wuyanshj na fitowa, da kyar jin tana neman mutuwa ta gyadamai kai da kyar, sakinta yayi yawuce gefe wani irin tari tafara kaman zata shura tunda take ba'a taba shaketa hakaba, juyowa yayi ahankali yana kallonta yana kokarin saita kanshi, dawani irin sauri yadawo inda take janta yayi zuwa jikinshi dasauri ta kwalalo idanu a tsorace danta zaci wani abun zaisake mata kawai yahada bakinshi da nata wani irin ajiyan zuciya yasauke kaman yadade daman yana neman abin yashiga kissing nata sosai yana sauke ajiyan zuciya yanadan groaning, yanda ya kankameta zaka dauka za'a kwace mishi itane, hannunshi na yawo abayanta kafin ahankali yadauke hannun nashi kan bombom dinta, wani irin matsawa yayi baisan lokacin dayace "auuuuchhhh Mmmnnn" yanda jikinta keda taushi haka bombom dinta shima yakeda taushi, knocking kofar lift din yaji anyi wata daga waje nacewa I think the doors sunyi jamming ne, gently yasaki bakinta batare daya cire fuskarshi dagakan nata ba yana kallon fuskanta yanda idanunta suke a lumshe jikinta ko'ina bari yake cikin wata yar kakkausar murya yace "take this as a warning" ko kwakkwaran motsi takasa hakan yasa yakai hannunshi yakama habanta yace "open ur eyes" idanunta tabude dasukai bala'in ja takallai harwani tsoron kallonshi take tsabagen yanda takara firgita dashi bakinta ne yashiga motsi sosai, bakin yabida kallo yace "say it" hawaye ne ya gangaro daga idanunta ahankali while her body still shakes tace "bazan karaba kayakuri please" wani mugun short smile yasakin mata batare dayay magana ba yasaki habanta sanan yajuya yana facing kofan, neck tie dinshi da riganshi yashiga gyarawa kaman baiyi komiba, batare daya juyo yakalleta ba yace "pick ur veil and cover ur hair" gyadamai kai tayi jikinta har tsuma yake ta tsugunna tadauki gyalen tahau nannaadawa tana rike hawayen dake zubowa ko akwai ta inda yake ganinta ne oho amman saida tagama nannade gyalen tsaf sanan taga yadanna wani boturi kofan yabudu dahar anje ankira security suna ganinshi duk aka shiga gaidashi. "welcome Sir, Good Afternoon Sir" ashaken nan ya amsasu batare daya kallesu ba yawuce abinshi zuwa mosque, shigowa wani guy wanda zaije sama yayi yanadan kallon Du'a ganin yanda idanunta sukai jajir ga hawaye yacika idanunshi, danna lift din yayi ahankali ta runtse ido, juyowa yayi yakalleta yace "are u scared of lift, is that why ur eyes are reddish"? Kaman zata gyadamai kai da sauri tai shiru tareda kawadda kanta gefe, suna kaiwa 5th floor tafito daga lift din kafinma shi yafito, bin bayanta yay da kallo yana murmushi yace "wow finally I get to see this damsel alone yau bata tareda M.D, kaman ma sunyi fadane, but guy! this girl fine finish wlh, God finish work for her body" wucewa office dinshiyayi yana kara kirsa yanayin ta a idanunshi. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 4️⃣8️⃣ Yau kiri kiri tunda ta tashi taji babu irin abinda bataso kaman taje aiki anything da zaima hadata da Asad yanzu batasonshi, kafin tafito saida Matar da aka Grandma takawo mata maisuna Jummalo tabata magungunan safe kusan kala hudu, sanan tadorata kan wani kujera ta rufa mata bargo ana turarata da hayaki saida aka gama sanan tabarta tafi ahankali take tafiya dakin Grandma tabude dasauri Grandma tajuyo tace "kece ke kamshi haka"? gyadamata kai tayi tana tabe baki tace "Grandma sai bani wasu magunguna take marasa dadi dan Allah tabari" haba Grandma tarike tace "dakinsan kudin dana kashe nadauko Jummalo dabakice hakaba yanaga baki shirya office ba" raurau tai da idanu tace "Grandma banda lpy bazan iya zuwaba please" dasauri Grandma tace "kinfi kowa sanin Asad Du'a tsakaninku keda mijinki" adan tsorace takama hannun Grandma tace "Grandma dan Allah kinji ki kirashi kigayamai banda lpy please" tai raurau da idanu kaman zatai kuka dayasa Grandma taji tausayinta wayanta tadauka tai dialing mata number Asad sanan tamika mata wayan tace "nidai kinga tafiyana gashinan ki gayamai" tawuce tafita daga dakin, ahankali tadauki wayan takara a kunne, ringing daya zuwa biyu Asad yadauka ahankali yace "morning Grandma" faduwa gabanta yashigayi da kyar ta iya daurewa tace "uhmm good morning Ya Asad" shiru yayi yanajinta baice komiba, murya chan kasa cikeda tsoro da fargaban abinda zaice mata tace "Ya Asad I can't come to office today banda lafiya" tai shiru, shiru shima yayi dayasa taciro wayan daga kunnenta takalla ganin still yana kai yasa tamaida wayan kunnenta, bata taba tsammani ko tunani zai tambayeta meke damunta ba taji ahankali yace "what's wrong with you" shiru tayi tama rasa mezatace, tunawa da kafanta da waist dinta na ciwo sabida faduwan dayasa tayi tace "my legs and waist" murya chan kasa yace "suke cewo" gyadamai kai tayi ahankali kaman yana gabanta tace "eh" katse wayan taji yayi batare dayace mata komiba, tashi tayi tareda murguda baki tace "ni wlh bazani ba ai nariga nagaya maka" contact din Grandma ta shiga tana addu'a Allah yasa tanada number Aneesha ganin, Aneesah yasa tai dialing number dasauri takara a kunne, wayan na gabda tsinkewa aka dauki wayan tace "Grandma ina kwana" muryachan kasa Du'a tace "Aneesah it's me, I am sorry" cikin wani irin fushi Aneesah tace "dan kutumar ubanki da uwarki dasuka tsaneki kada kisake kirana, bani baki Du'a baki bani, kin yaudareni and just watch out I am coming for u with full force" takatse wayan ahankali ta ijiye wayan gabaki daya batajin dadin fita daga dakin tayi kawai takoma daki ahankali taje ta kwanta kan gado. Grandma na zaune kan kujera aka bude kofa aka shigoda sallama, Asad tagani yana sanye da brown suit daya amsheshi, hakanan yau yaji yanajin kunyanta, wani irin murmushi tayi tace "Asad kodayake nace sirikina" daure fuska yayi yakaraso batare daya zauna ba yace "good morning" kawai ya ijiye mata wani leda kusada ita yajuya yafice yace "natafi office" daukan ledan tayida sauri ganin maganin joint irin na shafawan nan dana sha yasa tabude baki takai hannu tarufe saikuma tasaki murmushi kawai batace komiba tashiga kwalama Du'a kira. "Du'a Du'a" daga sama taji Du'a ta amsa sanan tasauko ledan Grandma tamika nata tace "gashinan mijinki yakawo miki magungunan ciwon dakika cemai kinayi amsa kije kiyi kari tunda dai kindage bazaki aiki yauba" hannu tasa takarba tajuya tai dinning itakuma Grandma tai sama dakinta tashiga tadanna ma Ammi kira. Zaune yake adakin lounge din dagashi sai boxer ga wata mace agefenshi tana bacci jikinta tsirara, ajiyan zuciya tasauke yadaura kanshi kan gado yanajin ihun abokinshi Senator Abuwa da tashi babe din suna sumbatu, tashi yayi ahankali yasauka dagakan gado sanan yakaraso wajen table din tsakiyan dakin yadau kwalin taba yabude yazari daya yadau lighter dake wajen yawuce yabude kofa yafice, gidane mai girman gaske da akayishi kaman hotel su sukasai abinsu sabida kawo babies dinsu, zama yayi kan wani swinging chair yana lilo akan kujeran yana busan taba yayi zurfi atunani, yana zaune saiga dayan kofan yafito abokin nashi yafito shima da gajeren wando sai uban katon ciki rikeda tashi karan ta an karasowa yayi yazauna kusada Dad yana washe baki yace "ya yarinyar nan dana baka ta iya harka kuwa" yatsine fuska yayi yace "balaifi at least naji dadi" yay maganan yana busa taba kallonshi abokin nashi yayi yace "wai meke damunka me kwanan nan Mijinyawa eh? Dukka dawo kaman bakaiba kai yaushi mata basa maka dadi wai duk sabida Zinariyan ka ta gudu ne" tabe baki yayi ya girgiza kai yace "wanan tun yaushe na manta da ita ta gudu saime anfasa harkan ne yammata nawa nahaka yanzu dabata nan wlh ba Zinariya bace matsalata ba matsalata daban ni" yanda yay magana yasa abokin yace "to talk to me mana bayau muka fara samo solution ba" dan shiru yayi yay jimmm kaman bazaiyi magana ba saikuma yace "is about my only Son Asad, ai kasan yanda tsakanina dashi yake, kwanan nan nasamu namai wayau ta hanyar nuna uwarshi ce komi na rayuwana nasamu yasoma kulani, kasan menene Bindi nafison Asad kan komi na duniyan nan amman na lura kaman Asad ne Jarabta ta billahillazi" Yay shiru yana hura iskan taba yace "shekaran jiya idanuna biyu fa kaman wanda akama asiri wlh danhar mamaki nake naje muka daurama Asad aure....." Nan yabashi labarin Du'a tass da yanda akayi akai auren sanan yace "kasan menene ni nasan Asad bayasonta, zanma iyace maka haryau baima yarinyan kallon da yakai na minti daya ba, baya kaunanta kwata kwata but kaman yanda kanwata Turai tafadi ne ba'a trusting namiji da mace, yanda yaga yanzu yazama mallakintan nan koda baison yarinyar nan zai iya kama yar mutane ya kwakule tass yaci ya danna mata ciki after all jinina ne ajikinshi kakuma sanni da gindi saidai in bansamu bane baxanci ba ina mai tabbatar maka idan Asad dakebe da yarinyar nan sai am kwashi yan kallo to kawai ni bansan yanda zan bulloma abin bane, kagane bawai auren yarinyar zanyi ba ko karaman yarinyar gidana Aneesah kenan ta girmi yarinyar tayaya zan aurota nakawo gida kagane, kawai dai sonake mushana tare na tsotse romonta tass, amman kuma tazama matar dana Asad sanan nikuma yanzu takai dako rufe idanu nayi ita make gani billahillazi kuwan" tunda yake maganan Abokin nashi ke kallonshi saida yagama tass yace "duk iskancin mu muyi muci karanmu ba babbaka amman karmu sake mu shigo gida zai iya tabarbare abu, ni naga danka Asad, ayanda yaron nan keda bakar zuciya billahillazi ko bayason yarinyar nan idan yaga karabeta wanan karan zai yafeka amatsayin Uba ne gabaki daya" dafa goshinshi Abba yayi yace "wlh nasani, kuma nasan koda nan gaba yasaketa naje ina nemanta yagane haka still sai munyi bace bace dashi, ni gaji jarababben son yarinyar nake kaman zan shura, kai kaga duwawun yarinyar nan kuwa da nono bura'uban chan, idan kaga dukiyan fulanin nata kaman an hura manyan balam balam guda biyu ansa mata a kirji gasu amugun tsaye, kugunta kaman pencil asalin takwas ce yarinyar wlh, yar shika har imagining nake yanda raminta zai kasance wayyo Allah na" yay maganan gabanshi natashi yakai hannunshi yakama sanan yace "idan kaga kyan yarinyar nan kai in karkema sabida kagane aljana ma ake cemata tsabagen kyanta dan tafi kama da aljanu bata kama da bil asama kokai kaganta saika kyasa" bugamai kafada abokin nashi yayi yace "this is a friendly advice, kaci kowace mace aduniyan nan is allowed bazan taba hanaka ba Abdullahi, amman matar yaronka tall da Allah yabaka aduniya inaaaaa!!! Kaduba kagani fa duk uban matan dakaci dakai kanka bazaka iya kirgawava Allah baitaba baka d'a ba kaiko bari ba'a tabayi akanka ba, this only one da Allah yabaka maintain a lifetime peace dashi, ko yanason yarinyar nan kobayasonta tunda dai ya aureta ta haramta agareka, ka kiyayi matar danka, tashi mukoma ciki kasa chaji dan gashinan dukka tashi nizan koma nai round 2 ne" yatsine fuska Dad yayi cikeda muguwan damuwa yace "barni anan katafi banjin sakeyi" wucewa yayi abinshi yabar Dad awajen sai tunani tunani yake ya kwance yahada ya kwance harya gaji yatashi yakoma ciki yaje ya kwanta ma yarinyar ta cishi sanan suka gama yaje yay wanka yazo yabiyata sanan ya shirya yay tafiyanshi. Duk suna zaune a dinning banda Asad dashi kadaine bai dawoba yawuce polo kallon match, Sharif ne kawai yadawo gida gyaran murya Dad yayi hakan yasa kowa ya kalleshi, Ammi yakalla sanan yace "inaso yarinyar nan ahnnn ahh Du'a tadinga shigowa kullum tana gaidamu, nasan dasafe tana tafiya aiki, but da yamma idan tadawo tazo nan gida sai bayan sallan Isha haka takoma gida, koya kika gani wife" wani irin hadadden murmushi Ammi tayi like she never expected magana haka daga wajen Dad, dasauri tace "wow wlh naji dadi sosai" baki Turai tabude zatai magana yadaga mata hannu yace "kinga Turai wlh banason damuwa, allow us to help this girl, koda nasan Asad Asad zai rabuda itane amman tashigo cikinmu mujata ajiki muzama family da batada shi kingane, koda wasa karki bari naji labarin kinma yarinyar nan wani abu idan tazo, daman that's all I wanna say zaku iya tafiya" Yay maganan yana tashi yawuce sama binshi Ammi tayi tana wani irin jin dadi aranta, tashi Aneesah dahar wata yar rama tayi tawuce fuuuu abinta. Zaune suke afalo danhar tai shirin bacci Grandma ta kwala mata kira tana sanye cikin wata cotton soft t-shirt na bacci burgujeje baki daya tsayamata aguiwa, gashin kanta abarbaje batai parking ba tazauna tanashan maganin da jummalo tabata a cup dazafinshi tana turo baki, budu kofan da akayi da sallama chan kasa yasa duk suka juyo Asad ne yana sanye da 3quatwr wando fari kal da farin riga da p-cap, da bakin glasses a idanunshi kana ganinshi kasan badaga gida yakeba, ganinshi yasa Grandma tai wani kalan murmushi aranta batare data nuna akan fuskanta tace "Asad kaine kafin kadamenida fitinan ka kaga Zola wuce katafi dakinka asama baki zan yanzun nan yan wajen aikina zasu cika falo, bari nasa Du'a takawo maka Coffee ko kozakaci abinci nasan bakacin abinci idan dare yay haka" yatsine fuska yayi ya girgiza mata kai alamun bazaici abinci ba yawuce stairs abinshi, wani irin murmushi Grandma tayi tana kara tabbatarwa so dagaske Asad nason Du'a this are all sign na soyayya amman dayake takadirin yarone shi ja'iri miskilin banza bazai nunaba, juyawa tayi takalli Du'a dake faman kurban maganin data gamasha tace "tashi akwai coffee a flask din gabanki kizuba kidauka a tray kikaima mijinki sama". 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️M SHAKUR EPISODE 4️⃣9️⃣ Wani irin faduwa gabanta yayi jin ankira shi mijinta itawai wayace musu mijinta ne barima taje zatamai maganan Allah yabata ikon yi, tashi tayi tadau mug din wajen ta tsiyaya coffee sanan tadaura a tray tadauka Grandma dake kallonta tace "kiyi knocking kafin ki shiga" Gyadamata kai tayi sanan tawuce saman tana tafiyan nan nata dake daukan hankali, hanyar lungun dataga yafito daga ciki ranan nan tayi kirjinta na dukan uku uku bin wajen tayida kallo wlh bata taba sani akwai daki awajen nan ba, knocking tayi ahankali akan kofan, wanan karan takai wajen 5min hartanaji kaman tajuya ta tafi abinta but tsoronshi yahata sanan taji da wanan shegen sigan maganan nan nashi yana ciccin kunu kaman ansashi dole yace "come in" yanda tagaji da tsayawa rikeda tray yasa bata bata lokaci ba ahankali tabude kofan tashiga ciki kanta akasa dakin sanyi gawani sassanyar kamshi na jikinshi da duk inda ya shiga sai kamshin yabude ko'ina, gadan duhu duhu da dakin yayidan wani kalan cozy wuta ya kunna da ita batamasan da kalanshi agidan ba sai adakin, dan table din datagani tawajen gadon ta ijiye tray din akai sanan tajuya zata fita tai wajen kofa, kofan ta taba jinshi akulle yaki buduwa yasa ta jijjiga ta murda ta murda but still a kulle, ahankali tajuyo da kanshi takalleshi kaman wacce ke tsoron kallonshi, mug din coffee da takawo taga yadauka yakai baki yana sipping yana daddanna wayanshi kaman baimasan ana bubbuga kofanba, adan tsorace murya chan kasa tace "zan fita" ko kallonta baiyiba yanda yake sipping coffee dinshi yana danna wayan abinma saiyay kaman baimaji tace zata fitaba, shiru tadanyi kirjinta na dukan uku uku still wondering shiya kulle kofan ko kofan ya kulle kanshi ko itace data shigo taje ta kulle bata saniba dan irin kofanta ne kofanta bata kulkuwanma mutu saidai idan kaika kulle, wasa tashiga yi da yatsunta tana kokanton yimai maganan amman takasa, dago kanta tayi ahankali dantaga koyagama shan coffee hada idanu tayidashi yana kallonta da mayun idanunshi dinan dakesa mutum shakkan shi, ahankali tasaukar da kanta kasa takai hannunta tanajan rigan jikinta kasa ganin kaman fararen kafanta yake kallo, daurewa tayi harda runtse idanunta ahankali cikin muryan bala'in tsoro da automatically yakoma na kaman karaman baby dake lallaba mamanta tace "Ya Asad uhmmmm Thank you for helping me yesterday" sanan tai shiru tana hadiye wani kullutu daya tsayamata awuya sanan tadago kanta takalleshi sake hada idanu sukayi still kallonta yake bayako kyaftawa, ahankali takai hannunta ta gyara kalban dasuka zubo ta gaban fuskanta suka rufe mata idanu takaisu gefe sanan tashiga wasada yatsunta murya chan ciki datafi na dazu kankancewa tace "Ya Asad uhmmmm kaga su Abba sun koma basu tafi dani ba shine nakeso muraba auren ko, kagama saisu Grandma da kowa sunsan it was not a real marriage, kawai kayi hakanne to save me, inyaso nan gaba nasami miji sainai auren gaskiya abuna ko"? Takarashe maganan ahankali, jin shiru baice komiba har kusan 5min yasa ahankali tadago kanta still Kirjinta na dukan bakwai bakwai ganin babushi akan gado sai wayanshi da screen din ke haske hakan yasa kawai ta firgirce kafin kaceme kawai taga dakin yay duhu sosai, zabura tayi tajuya tanakai hannunta jikin kofan tana neman handle tamurza tajiko Allah zaisa yabude tafice kawai taji ankama hannunta an mugun fisganta, baki tabude zatai ihu. "Gran.........." wani irin kaima bakinta duka yayi dayasa tahadiye maganan da sauri cikin huge voice yace "ko tari kikai anan saina babballaki" da kafanshi yasa yawani irin tokareta tai baya hartasa rai xatajita akasa tajita tafada kan gado kafin tamayi yunkurin yin kyakkyawan motsi tajishi gabaki daya yafado kan jikinta yasakin mata nauyi, wanan karan fashewa tayi da kuka sosai jikinta na bari ko'ina, hucin dayake kadai yatabbatar mata ranshi a bala'in bace yake, fashewa dakuka sosai tayi muryanta baya fita sosai tace "Ya Asad dan Allah kayakuri wlh wlh wlh bazan kara maka maganan ba, dan Allah kaji dan Allah, Allah na rantse maka bazan kara maka maganan ba, dan Allah wlh duk lokacin da kaga dama karabu dani na yarda dan Allah kayakuri natuba" yanda tarude har a heart beat dinta yakejin rudewan, hannunshi yakai yakama habanta da karfi abin yamata zafi sosai cikin wani irin thick kakkausar murya yace "did u just tell me zaki auri wani"? Girgizamai kai tayi tana rushemai da kuka sosai tace "badakai nakeba, ba abinda zan fadi kenan ba mistake ne, kayakuri baran karaba" murya chan kasa yace "OH yes I will make sure now bazaki karaba" yay maganan yanakai fuskanshi saitin nata ta yanda har hucin numfashin shi tanaji kan fuskanta yana kallon kwayan idanunta dake kyalli sosai sabida yanda ruwan hawaye yacikasu yace "stop crying for me kona zaneki" hadiye kukan tai gam tana nishi sama sama, lumshe idanunshi yayi yana shakan kamshin breath dinta dakeda calm nature, kafin ahankali yasaukar da bakinshi kan hancinta yamanna ma hancin kiss kadan ahankali yace "shiiiiiiiiiiiii" gyadamai kai tayi tana numfashi da sauri dasauri jin katon namiji akan jikinta ya danne ta, sanan yacire bakinshi daga hancin yadaura kan bakinta, wanan karanma saida yasake sakin ijiyan zuciya feeling her soft lips dakenan very warm and soft, lasansu yashigayi kaman wanda ke lasan minti mai tsinke sanan yawani fizge bakinta da karfi yashiga kissing yana kara matseta da karfi kaman zai karyata yana nishi mai kara. "uhnnnnnnn, Hmmmmm" Tundaga yatsun kafanta har zuwa tsakiyan kanta takejin wani irin sanyi sosai na shiganta, gawani kalan tafiya kaman na tsutsa yana kwana kwana yana zagaye zagaye acikinta takeji, bakinshi is damn sweet acikin nata that I cannot lie about it or deny, yanda yake nishi yana groaning a bakinta datakeji har cikin tsakiyan kunnenta yanasata feeling very weak kaman ta kankameshi as a support takeji dan she's loosing her strength, her body is all weak, motsi da kafanta tafara tana lumlumshe ido tanaso tai magana takasa, jin jikinta yadauki wani irin total shock yasa batasan lokacin data daga hannayenta dake gefen gado tadaura abayanshi ba ta kankameshi sosai, hakan datayi yasa taji yanda yake ihun yaragu saikuma ahankali taji yay shiru yasaki lips din nata ahankali tareda sakin ijiyan zuciya, gently taji yana rage nauyin dayasakin mata ajikinta saikuma ahankali taji yatashi daga jikinta, kankame idanunta tayi da jikinta, jin karan yabude kofa yasa dagudu tabude idanunta danta dauka kofan fita yabude ganin bathroom yabude ya shiga yasa takai hannu tashare idanunta dasuka zubo da kwalla sanan tadaura hannun kan bakinta, lips dinta harwani zugi suke mata jitayima sun kumbura, wai menene haka yake mata ne eh, she hates it with passion, jin yana kokarin bude kofan yasa dasauri tamaida idanunta ta datse dan bazata iyama kallonshi ba. "Stand up" taji yafadi calmly, bude idanunta tayi ahankali hada idanu sukayi dashi yana tsaye akanta ya kunna full light na dakin yana kallonta, idanunshi sunyi ja sundan kankance kaman baida lpy, ahankali ta sauka daga gadon tamike tsaye kanta akasa, jitayi kawa yadauketa yazaunaar da ita kan gado dasauri ta kalleshi hada idanu sukayi yana kallon fuskanta, juyarda kanta tayi da sauri dan bata iya jure kallonshi, gani tayi ya tsugunna agabanta sanan yakai hannunshi ahankali yakama kafafunta duka biyun yana kallonsu, juyoda kai tayi takalleshi gannin hankalinshi nakan kafanta yasa tacigaba da kallonshi tana mamakin maiyakeyi, right leg dinta ya ijiye akasa sanan yarike left din, kafin yamika hannu yadauki wani dan box da tunda tashigo dakin taganshi akan side drawer batasan meba yabude, wani balm tagani a box din lakatowa yayi yakai wajen guiwanta yashafa sanan taga yadaura hannunshi kan guwiwan ya murza, wani irin zabura tayi zata mike dasauri yakalleta fuska adaure yace "don't try that" gyadamai kai tayi jikinta narawa, ahankali ya shiga liliya wajen runtse idanu tayi tana kuka ahankali chan batasan meyayi ba taji guwiwan yay mata wani azababben zafi dayasa tafashe da kuka sosai tana ihu saikuma taji guwiwan yay kass, sanan ya ijiye guiwan yadaga kanshi yana kallonta, kallonshi tayi ahankali tana kuka sanan takalli guiwan tanakai bakinta wajen tana hurawa gashinta na lilo both side, tsareta a idanu yayi ahankali yace "does it hurt" gyadamai kai tayi ahankali tana goge kwalla da bayan hannunta tana hura guiwan dan abinda yashafa mata kaman barkono harcikin bargonta takeji, hannunshi yakai gently yakama gashinta dake lilo dasauri tadago kanta takallai hawaye sun cika idanun, ahankali yana kallonta yatattara kitson yakai gefen kunnenta ya sagala awajen, maida idanunta kan gwuiwan tayi tana hurawa still. Tashi tsaye yayi yazauna gefenta kan gadon dasauri tadago da kanta takalleshi, wayanshi taga yakara akunnenshi kaman waya yake amman baya magana but tana iyajin sound na magana dagata dayan gefen, ahankali take binshi da kallo tundaga kan fuskarshi har zuwa kan kirjinshi dayabar boturan abude ganin tulin kwantaccen bakin gashi yasa dawani irin sauri tadauke kanta dan batasan namiji nada gashi ajikinta hakaba, kaman asiri jitayi tanaso tasake ganin gashin dan gani tayi kaman idanunta ne amman ba gashi bane, ahankali tasake juyowa fuskanshi takalla ganin ya lunshe idanunshi yana sauraron maganan da akemai yasa ahankali tadan dukarda kanta tana leka leken gashin kirji daga inda take zaune, wani dan gajeren murmushi ne yasaki batare daya bude idanunshi ba dan duk abinda takeyi yana kallonta kafin ahankali yakai hannunshi daya yakama side da side din rigan yahada tarike a tsakiyan sabida tadena ganin kirjinshi dawani irin sauri takalli fuskanshi, ganin har lokacin akulle yasa tasauke ijiyan zuciya takoma gefen datake tazauna da kyau tana jingina da bangon gadon, ahankali taji yafara magana da harshen turenci calmly yana maganan one one daga yanda maganan da abubuwan dayake cewa tagane it's a business related call. Gabaki daya tagaji ga wayan yaki karewa sai magana yake ahankali akuma natse kaman ba jiranshi take yabude mata kofa tafita ba, kwasheta bacci yayi azaune awajen yanda duk ta takure jikin bangon gadon tana turo baki, jin yadenajin yan motsi motsinta yasa yadan juyo yakalleta, ganin tai bacci makure zaune akan gado yasa ahankali ya gyara zama yanda zaiyi facing nata yana kallonta, she looks so innocent, ga dan bakin nan nata data turo, ga kalban dasuka zubo agefen fuskanta binsu yay da kallo yanda har cinyanta tsayin gashin, yanda tazauna yakebi da kallo da wayan nan white leg din nata, gently idanunshi suka sauka kan white pantie dake jikinta dawani irin sauri yadauke kanshi dan rigan datasaka iya cinyanta ya tsaya yanda take baccin atakure yasa taidan wawan zama dayake iya hango white lace pant din dake jikinta mai bala'in kyau. Wani irin gasping breath yayi he can't believe what he just saw, tambayanshi abu ake a wayan amman yakasa bada amsa, ahankali yasake juyoda fuskanshi wanan karan sosai idanunshi suka sauka awajen, he p*s yacika wandon ga shaidan jikewa, dawani irin sauri yasauka daga gadon jin jikinshi yasoma tsuma baison abinda zaisa yayi abin kunya agidan Grandma bude kofa yayi yawuce yafita, wayan ma kasa gane abinda ake fadi yayi hakan yasa ya katse wayan kawai yatura wayan aljihu yasauka kasa, ganin babu Grandma a falo bakaramin dadin abin yajiba dasauri yawuce yatafi gida abinshi gabaki daya hankalinshi yatashi he's way too Horny. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR EPISODE 5️⃣0️⃣ Wuraren 3 na Asuba tafarka daga baccin daya kwasheta ganin inda take yasa tabi ko'ina da kallo ganin baya dakin yasa dasauri tazabura tasauka daga gadon taiwajen kofa tana taba kofan taji yabude harda gudunta takwasa ta tafi dakinta, kwanciya tayi tacigaba da baccin ta ana kiran salla ta tashi bayi tashiga tazo tai salla tazauna ta gyara haddan ta sanan ta tashi lokacin gari haryay haske, bude kofa Grandma tayi tashigo, baki Du'a tabude zata gaida Grandma ta tareta tace "ki shirya kitafi wajen aiki bazaki zauna min agida yauba ehe" turo baki tayi tazo gaban Grandma shigewa jikinta tayi ashagwabe tace "har yanzu banda lafiya fa" turamata hanci Grandma tayi tace "sake ni naje nai lazimi nidai" sakinta tayi Grandma tawuce tafita babu yanda ta iya bayi ya shiga tayo wanka tafito shiryawa tayi cikin wani mustard abaya sanan tasauko kasa bintada kallo Grandma tayi, zama tayi tai breakfast tadanci abinci sanan ta tashi tana kallon agogo 8 saura minti 15, tsayawa tayi gaban mirror falon tai rolling gyalenta tai kyau sanan tazo cikin falon bye Grandma, daidai lokacin security gidansu yay knocking, isowa Grandma tamai hakan Yasa yashigo rikeda leda Du'a ya kalla yamikamata wata yar milk color paper jaka yace "gashi Mr Asad yace nabaki" kallonshi Du'a tayi takalli ledan a little bit confuse, dasauri Grandma tace "karba mana mijinki ya aikomiki da abu kin tsaya turus kina kallonshi" ahankali tasa hannu ta amsa security yajuya yafita, bude wayan tayi ganin kwalin waya iPhone 13 pro max irin nashi yasa Grandma kawai tai murmushi tace "daman wani zai siyamiki saisa ya karbi wanchan ai yayi kyau" bude kwalin tayi taga wayan a kunne da Sim ajiki, Grandma dake kallonta tace "kinga sa wayan nan ajaka kikakai office kya kalleta da kyau karki latti" saka wayan tai ajaka tawuce tafita, gaida direban Grandma tayi sanan tashiga baya aka bude musu gate suna fita motan gidansu Asad suka gani pake kofar gidan bude motan akayi taga Aneesah tafito tasaka wani red atampa tai kyau sosai tana dagama direban hannu alamun ya tsaya hakan yasa ya tsaya, faduwa gabanta yahauyi sosai amman dai ta daure tana kallon Aneesah natahowa, tana zuwa bayan motan tabude tana kallon Du'a data juyo tana kallonta atsorace kana ganin idanunta kaga tsoron, ga mamakinta saitaga Aneesah tasakin mata murmushi tace "kinsan kinmin laifi shine kika dena shigowa gidanmu ko kinma kashe wayanki bana iya kiranki eh Du'a"? Tai maganan tana murmushi sosai, ahankali Du'a na kallonta cikeda tsoro tace "kiyakur......" hannu Aneesah takai tadaura kan bakinta tana kallonta tace "tsakanina dake babu ban hakuri Du'a, hasalima nine yakamata nabaki hakuri I was so angry naje inata crazy things a group sorry kinji Du'a wlh bakimin komiba, mun shirya" dawani irin sauri Du'a ta gyadamata kai tana murmushi, murmushi itama Aneesa tayi tace "ina zaki"? Ahankali tace "office" dasauri Aneesah tace "zomuje ta motan mu muyi hira mundade bamu hadu ba ai duk hanya dayane" dan kallonta Du'a tayi kaman tanaso tagano wani abu, hannu Aneesah tamika mata tana murmushi tace "wuce mutafi tare, Uncle munhutasheka kagayama Hajiya mune yau zamu sauketa a office saimu wuce school" dariya direban Hajiya yayi yace "tom shikenan" kallon Du'a tayi tace "let's go kawo jakanki na rikemiki" karban jakan Du'a tayi, ahankali Du'a tasauko, Aneesa tamaida kofan tarufe sanan tabata jakan takarba ta sagala a kafada sanan suka wuce motansu suka shiga, Mariya kadai tagani a motan itama murmushi tama Du'a, zama Du'a tayi suka sata atsakiya sanan direvan yajasu suka tafi shikuma direban Grandma yakoma gida. Hakanan tunda tashiga motan taji zuciyanta na bugawa bam bam bam amman tadai daure, itadai Mariya tai shiru danne dannen wayanta take abinta itakuma Aneesah sai janta da hira take tana mata nodding kai batare datai magana ba ahaka har sukakai Nile takasa magana, parking direban yayi bude mota Mariya tayi tajuyo takalli Aneesah tace "natafi class" gyadamata kai Aneesah tayi sanan ta taba Du'a tace "tashi muje" kallonta Du'a tayi kaman mai shakkanta takasa cewa komi tafito, Aneesa ma tafito tacema direban "Bala katafi saikuma idan muntashi" to Hajiya yaja motan yatafi, sanan takalli Du'a takama hannunta tace "zomuje kiga school dinmu sai in kaiki office nasan bakisan hanya ba" ahankali tana binta suna tafiya tace "zanyi latti" danjuyowa Aneesah tayi takalleta tace "munma kai" wajen wani red car dake pake sukayi, gani tayi Aneesah tabude mata baya tace "shiga" ahankali ta shiga, sanan itama Aneesah tashiga tarufe kofa takalli kawayen ta wasu classic yammata dake gaba manya, mai tukin na sanye da atampa dayan na sanye da english wears tace "let's go girls" suka kunna motan sukaja, hira duka suka shiga yi suka shareta dayasa taji she's so uncomfortable, matan biyu sai kallon Du'a suke ta mirror, ganin instead of su yanki titi sun yanki dajin wajajen hanyar Nile ne yasa tajuyo takalli Aneesah lips dinta har rawa suke ahankali tace "Aneesah ina zamu" wani irin murmushi Aneesah tayi takalli kawarta dake tuki tace "Zeezee ana tambaya fa wai ina zamu" juyowa yarinyar tayi tana tuki takalli Du'a sanan tai dariya tace "zamuje muci ubanki HOD ne fine girl, sounds fun right" suka wani kwashe da dariya dukansu ukun harda Aneesah, kuka da tsoro dukane taji yazo mata amman tadaure takalli Aneesah dake dariya har lokacin tace "Aneesah dan Allah ki saukeni anan natafi office Ya Asad zaimin fada nai latti" tsayarda dariyan da Aneesah keyi tayi jin yanda tai maganan Asad din batai wata wataba kawai ta kwasama Du'a mari jikake pauu! ihu yammatan gabangaban motan suka hauyi dayan da suke cema Billy tace "Fine girl akama marin nan Zeezee" dasauri Zeezee dake dariya tana tuki tace "ita akamawa fa, kuma kaman ya shigeta those her white eyes kaman gajimare sunyi jajir, welldone Aneesah marin ya shiga" murmushi Aneesah tayi tana hararan Du'a dake kallonta tana shafa inda ta mareta idanunta sunyi jajir, tace "wai har yanzu bamukai gidan bane muyi muje mubama hammata iska" wani irin kara gudu Zeezee tayi tace "in the next 1min ur majesty" murmushi sosai Aneesha tayi tanajin dadin yanda kawayen ta ke hyping nata tana karkada kafanta, daidai nan sukakai wani gida mai kama da gidan gona a tsakiyan dajin babban gida sosai, parking sukai akofar gidan sanan Zeezee tafito itama Aneesah tafito sanan taduka takalli Du'a dake zaune tace "Malama fito ko nasa afitomin dake" dasauri su Zeezee da Billy sukazo gaban kofan datake suna gyara hannun riga sukace "ashirye muke" bude kofa ahankali Du'a tayi tana rikeda riganta tana fitowa kawai da Billy da Zeezee suka ja hannayenta tana kokarin fizgewa amman taki suka bude gate suka shiga da ita babban gidan gonan ga katon compound suka wurgata tsakar gidan mugun fadi tayi milk color riganta yabaci, ahankali ta tashi tamike tsaye tana rikeda jakanta idanunta sunyi ja sosai amman taki kuka, Zeezee tagani da Billy sun zauna kan kujerun katakon dake kan dakali dakeda rumfa, sundauki wasu robobi da cokula sukahau bugawa kaman Ganga sanan sukace "zaki iya shigowa Aneesah" turo gate din Aneesah tayi tashigo sanan tamaida gate din tarufe tasaka sakata sanan tashigo ciki kan dankalin taje ta ijiye jakanta da wayanta sanan tadawo filin inda Du'a take atsaye tace "sabida kinga kinada kyau kinfini kyau kinada nono da duwawu da flat tummy wanda all yammata yanzu sunsan abinda maza keso kenan saisa kika kwashemin saurayi Du'a kikamin snatching" ahankali Du'a da idanunta sukai jajir sunsoma cikowa da hawaye tama rasa mezatace tace "kiyakuri Aneesah" ihu sukayi sukace "one zero, Aneesah kinci this round, the poor girl ta tsorata harta soma baki hakuri" wani irin murmushi Aneesah tayi feeling confident tana karajin kanta na kumbura sabida yanda kawayenta ke tunzurata, hannu biyu Aneesah tasa tace "you are nothing Du'a but a bad luck, bantaba ganin munafukan yarinya that hide behind pretty irinki ba, I regret saninki, Du'a inason Asad kaman raina kinsan shekara nawa nayi ina sonshi? Tun ina yar yarinya, tunda nafara wayau nasan Ya Asad nake sonshi amman tashi daya kin kwacemin shi kin aure sabida kinga kinada kyau u can steal any man eh, to bari kiji wanan kyan dakike tagama dashi sainai buzu buzu dashi yau wlh I will beat u blue black" Du'a na kallonta still har lokacin ahankali tace "Aneesah nidake kawayene fa, nima badason raina na aureshi ba kuma nace kiyakuri, nima banasonsh......" bata karasa maganan ba Aneesah tasake wanka mata mari akaro nabuyi habawa sai dariya da kida wajen su Zeezee sunama Aneesah welldone welldone dayasa Du'a taji kuka yazo mata gadan gadan amman tadaure but saura kiris tasaki kukan, Aneesah ta nunata da yatsa tace "wlh yau nakara yarda munafuka ceke makaryaciya kuma, bayan Dad yacemana kece kika ce shi kikeso shi zaki aura shine yanzu kike cewa baki sonshi, yanzu nake ganin dalilin dayasa yan uwanki basa sonki Du'a, no uwarki da ubanki ma basa sonki, u are just a p*ssy yarinyar nan, banza kina takama kinada kyau bakisan duk wanda yaga kyanki tausayinki yakeji ba sabida ansan this is not a normal kyau aljanna kawai mayya I am sure maitanki kikama Ya Asad kuma yau zan kwanceshi mayya kawai, mayya aljana" fashewa da kukan datake rikewa tayi tana girgizakai tace "niba mayya bace Aneesah kidena cemin mayya kuma Abba da Mami basu tsaneni ba, stop calling me with that name" tsit kakejin kidan dasukeyi sun dena Billy ta kalli Zeezee tace "she just replied Aneesah fa" Zeezee tace "Aneesah tsayawa kikayi kina kallonta ta mayarmiki da magana mai daci haka" kaman jiran maganan su Aneesa take aiko tai wani tsalle saikan Du'a tahau kimar Du'a dake kuka sosai tana ihu, ko kadan Du'a batasan yanda ake fadaba, kidan Zeezee tabarma Billy tadau wayanta tashiga recording tana dariya tace "goo Aneesah yauwa yimata lilis joints dinta zaki dinga duka da wajajen kayan alatun damage her face" ganin Aneesah na neman saka mata hannu a idanu gatada kumban kari datayi na birthday nada ta ture hannunta tana kuka sosai tarufe fuskanta gwanin ban tausayi, ita kanta Aneesah karfinta yakare ma wajen dukanta dan duka ba'a maidamaka da martani is tiring, taji duk gabobin jikinta sun sage amman taki denawa sabida yanda kawayenta ke hyping nata, Zeezee tace "sumarda ita ga tabarya chan" dagudu tasaki Du'a tai wajen tabaryan zata dauka kenan wayanta yashiga ringing dasauri tai wajen wayan tace "wake kirana" ganin yan ajinsu ne yasa tadauka, dagokai tayi takallesu tace "test wlh" dasauri suka yarda robobin kowa yadau jakanshi Aneesah ma tadauki nata duk sukai gate, juyowa tayi takalli Du'a dabata motsin kirki akasa tajuya takalli Zeezee daharta fita tace "wanchan banzan fa" hararanta Zeezee tayi tace "dalla muje muyi test muka dawo masan yanda zamuyida ita" fita tayi daga gate din sukaja gate din da kyau sanan suka shiga mota suka tafi. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR wa.me/+2347012181461 DUK WACCE TA KARANTA BATA BIYABA BAN YAFEBA, THIS BOOK IS 500 PAY INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK. EPISODE 5️⃣1️⃣ Wani kalan gajeren suma tayi tana nishi sama sama saikuma chan tabude idanunta batasan ya akayi ba ita datasan dasafe sukazo wajen nan gani tayi rana yasoma sauka komi najikinta ciwo yake mata kaman ba jikinta ba, kokarin tashi tayi amman taji takasa moving leg dinta hakan yasa da kyar ta karkata kanta takalli kafan dataji takasa motsi dashi jini tagani sosai akasan wajen kafin takalli kafan nata ganin kafan tayi kan wani katako da kusa biyu ke jikinshi kafanta na kanshi kusa biyu sun chaki kafanta sun nutse duka aciki, wani irin fashewa dawani mugun kuka tayi danji tayi tabama kanta tausayi wanan wani kalan rayuwa ne? Eh thought she will forever be happy awanan Abujan, who will save her anan tsakiyan dajin ya taimaka mata ko rarrafene tayi ta tafi gida, da kyar ta iya buda baki tadanyi ihu cikin kuka tace "ataimaka min dan Allah" ko motsi bataji sai kukan tsuntsaye danda alamu gidan gonan ma abandon one ne dan babu wani abin arziki aciki, sake dagokanta tayi kadan ta kwala ihu. "ataimaka min" wani kalan tsoro taji yana shiganta dan tasan a daji take tafashe da kuka sosai... Wasu gayune su hudu ke tafiya rikeda gorunan coke amman duk maihankali ya kalli goran ya kallesu yasan ba coke bane acikin goran ba idanunsu yay jajir suna tafiya suna layi, gasunan looking neat dan kana ganinsu kasan ba all this almajiran masu shaye shaye bane, kaman daga sama sukaji ihu ataimakenin Du'a duk tsayawa sukayi suna kallon kansu, daya daga cikinsu yace "kai Baaba na kwale ne koko da gaske ihun yarinya naji" atare sauran sukace "baka kwaleba Baaba muma munji" kalle kallen wajen suka shigayi suna layi dan abuge suke dukansu kafin su sakejin ihunta akaro nabuyi nan suka shiga neman saitin inda sukejin ihun. Jin tayi ihu tayi tayi amman babu alamun mutum yasa tashiga kalle kalle dan hakanan wayanta yafado mata arai, hango jakanta gefe tayi kayan ciki ma sun barbaje wayanta data hango agefe daban yaja tamika hannunta daya bala'in sage da kyar tana kokarin taba wayan baikai ba, fashewa da kuka tasakeyi sanan tasa duka karfinta taja jikinta da karfi wani irin fashewa tayida kuka takalli kafanta dake datse da katakon kutsan dake bulbulo bulbulo da jini sabida moving jikinta da tayi sanan tamikar da hannunta cikin ikon Allah hannun yakai wayan ahankali tadauki wayan sanan takoma ta kwanta flat, kasa daga wayan da kyau tayi ta kalla, saida tasake bata lokaci sanan tadaga hannunta tabude wayan da babu password tashiga keypad tana tunanin wazata kira watakeda number shi dan wanan sabon wayane, ijiye wayan tayi ahankali tasake fashewa da kuka dan hannunta yasake sakewa, ahankali tasake daga wayan wani zuciyan yabata data duba contact maybe tanada number dubawa tayi taga number daya kachal ne awajen da akai saving da emojin rings guda biyu, dialing number tayi takara a kunne tana runtse ido dan ita kadai tasan kalan azaban datakeji, wayan na gabda katsewa akai picking, cikin kuka sosai da muryanta dabaya fita sosai tace "Ya Asad kaine"? Batare daya amsa tambayanta ba strickly yace "what happen to your voice" wani irin ijiyan zuciya tasauke jinshine tace "Ya Asad bansan inda nakeba ina cikin daj......." daidai nan aka wani irin buga gate din da karan yasa ta firgice tasaki wayan takalli gate din dasauri, maza hudu tagani da gorunan coke a hannunsu idanunsu sunyi jajir suna layi suna kallonta dukansu suna bangaje juna suna dumfaro ta, daya daga cikinsu cikin muryan shaye shaye yace "kai Baaba mace yar shila nake gani haka akasa gasasshiya Allah ya ijiye mana ita mu kora da ita saman codeine dinan damukasha da harizona Baaba ko idanuna ne kemin gizo" dayan na gefensu dahar ya iso gabanta ne yaduka yana rike guiwanshi kaman wanda zaiyi ruku'u yana kallon Du'a cikin muryan maye yace "ehh wallahi Baaba kuma chakwai take" yakai hannunshi yashafa fuskarta dayaji fatar taushin tsiya kabarda hannunshi tayi tace "don't touch me, dan Allah kuciremin kusan nan daga kafana" karasowa sauran sukayi duk suka duka suna kallonta kaman basu taba ganin mace aduniya ba, yanda suke kallonta ga warin shaye shayen dasukeyi yasa tama fashe da kuka sosai. Tsaye yake yana karban wasu files dayasa akamai printing kaman ance yajuya yaga Asad nafitowa daga elevator daya bude ranshi a bala'in bace ga waya kare a kunnenshi, faduwa yaji gabanshi yayi ganin yay hanyar fita yasa yabishi da sauri yana kiranshi. "Asad Asad ina zaka, Asad" ko kulashi baiyiba yay wajen motanshi zai bude kenan Sharif yasha gabanshi yace "Asad bakaji ina maka magana bane I said what is wrong"? zare wayan yayi daga kunnenshi yamikama Sharif dasauri yakara wayan akunnenshi kukan Du'a yaji da muryan maza da su kansu awaya sunji yanda mazan suke abuge, dasauri yakalli Asad yace "ina Du'a taje data hadu da yan shaye shayen nan"? kasa magana yayi tsabagen yanda ranshi ke tafarfasa hakan yasa yace "kaga Asad zauna" yay maganan yana zaunar da shi sanan yakatse wayan yace "Du'a is using iPhone ko I can track her" wasu gurare yashiga a iPhone din Asad cikin 5min yace "got it let's go" zagayawa yayi yashiga dayan bangaren Asad yakunna motar yajata dawani irin mahaukacin gudu, Sharif yace maiyakai Du'a tsakiyan daji haka da babuma gidaje. Tsugunnawa duk sukayi akanta yanda kadai suke kallonta kaman sunga wata gasashiyar nama yasa Du'a take kuka sosai tace "dan Allah kuyakuri karku min komi" hamma daya daga cikinsu yayi yace "Baaaba nifa sonake nasa chaji awajen nan fa daman asama nake wlh" dasauri dayan yamike yana zare belt dinshi yace "ai wlh baka isaba nina farajin ihunta dan haka nizan fara saka chaji" na ukun ne yamike yace "kunga kuna harkan karanta dallah, daga ganin yar shilan nan bata tayi to miyene kuke wani rawan jiki, dukanmu zamusa chaji muyi gaba abinmu yan uwanta sazo su tsinceta ahaka bayan munsassaka chaji munyi full 100% mubarar da ita a achan bayan katangan gidan, amman yanzu shi Gwaska shizai fara tunda shi yafarajin ihunta yakuma ce mushigo gidan nan ba rushing mukadaine acikin dajin nan mukai hakuri kowa zai saka chajin" hakura sukayi shikuma wanda aka kira da Gwaskan kaman jira yake ya tsige belt ya yar yacire rigan jikinshi ya yar ya zare singileti shima ya yar sanan yazage zip din wando yaja wandon kasa, yarage dagashi sai dan gajeren wando, ihu Du'a tayi tana kuka sosai tana kokarin Jan jikinta baya kafanta na fito da jini, tsugunnawa Gwaskan yayi akanta yana murmushi sanan yakai hannunshi yawani finciki gyalen datai rolling dasaita yajawo da kanta sama sanan gyalen yacire kanta yakoma yabugi kasa kuma dayasa tai wani wahalallen kara. "durun uwa salatin arna! gashinta ne haka Gwaska" murmushi yayi yana bude goran coke din yadaga yakai baki yashanye sauran abin ciki duka sanan ya yarda goran yakai hannunshi zai taba kan Du'a tabude hannun tace "karka tabani" "Baaaba mai gardama ce wanan fa asamata karfi" "yanzu kuwa" yatashi yatsaya akanta yasata a osinshi sanan yakai hannunshi zaisa agaban riganta........ Kwanan shiga dajin Sharif yanunamai yace "we are going straight anan nake ganinta" shiga dajin Asad yayi da mahaukacin gudu amman ko mutum daya basu ganiba gadai alamu signal dinta suna gani amman basu alamun akwai mutane awajen nan ba gashi yamma tasomayi dan biyar saura, sunyi tafiya sosai suka fara hango wani old building mai gate dasauri Sharif yace "I think that's where she is"....... Kabarda hannunshi tasakeyi hakan yasa yace "Ke ni kike kabarwa da hannu" dasauri sauran sukace take hannun Baaba muga karshen tsiyanta, hannunta yakama yakai kasa yasa kafanshi yatake dayasa tai ihu sosai sanan yakai dayan ma kasa yatake sanan yakai hannunshi gaban riganta wajen biyun jikake kiiiiiiiiiiii ya barka rigan daidai an buga gate din anshigo dayasa dukansu suka juyo hardashi dake kan Du'a, Asad da Sharif ne suka shigo atare sunabin kowada kowa da kallo one by one kafin idanunshi su sauka kan Du'a dawani gardi ke tsaye kanta ya duka yana barka mata riga zuwa ciki ga black foamless bra na lace datasaka dayay parking boobs dinta da kyau tana wani irin kuka sabida yanda guy din yatake hannayenta, kallo daya Sharif yama side dinta baikaramata na biyu ba, Gwaskan dake tsaye kan Du'a ne ya kalle maza biyun dasukaci uban suit kaman masu aikin banki ne dasuka shigo gidan cikin muryan maye yace "kai dan gutsun uwarku kubar nan kuje kusami wani ginin kuje kuyi shaye shayen ku achan munriga mundau wanan" wani irin zuciya yadebi Asad wanda shi kanshi bayason yana irinta dan illata mutum yake kawai yaykan Gwaska dahar gyara tsayuwa yake akan Du'a yace "Au zoto abama hammata iska" Asad na zuwa baiyi wata wataba ya dunkule hannu yadaki kashin wuyanshi jikake kar wuyanshi ya karye, zai fada kan Du'a yawani dagashi da hannu daya yabuga abango sanan ya matsemai wuya kaman zai kasheshi, yana kakarin mutuwa idanuwanshi kaman zasu fito, ihu sauran sukayi zasuyi kan Asad dakecin uban Gwaska Sharif yataresu da nashi dukan yana barar dasu danko kadan babu karfi a jikinsu sabida yanda sukai shaye shaye kana dukansu suke barewa, idanda zakaga fuskan Asad zaka gudu makureshi sosai yayi cikin wani irin voice yace "how dare you touch my wife haaaaa!" kwalalo idanu Gwaska yayi kaman zai mutu amugun zuciye Asad yakama hannunshi yalumasu a idanunshi yace "saina tsiyayar da idanun daka kalleta dasu" sosai Gwaska yay ihu jin azaba a idanunshi, sanan Asad yawani irin gwara kanshi da bango ya barar dashi awajen assume ko motsi baiyi sanan yay inda Du'a take a kwance tana kuka takasa daga hannunta daya take akasa, jacket dinshi yacire dasauri yadagata yana kallonta yarufa mata akirjinta sanan yasake kwantar da ita ahankali, yanda yake abu zakasan amugun rude yake, gate yayi yafita da gudu booth dinshi yabude yadauko wani first aid kit dayake dashi yadawo ciki daidai Sharif yagama barar dasu yabiyo Asad din dagudu, kafanta da kusa kekai yabama Sharif yace "hold this kaga" karban kafan yayi da sauri yana kallon Du'a da idanunta ke kukkullewa kaman zata sume Asad shikuma yashiga bubbude komi na akwatin yana hadawa agefe sanan yadau wani ruwa yazuba akan ciwon, ihu tayi tana kokarin kwace kafan daga hannun Sharif dayaki saki, kafin yahada wani allura yamata sanan yakama katakon yatattaba jikin kafan kafin yafara pulling dinshi ahankali ihu tafara, taiwani juyi dayasa jacket din dayarufa mata yafadi tsayarda abinda yakeyi yayi da sauri yatashi yadau jacket din yasake rufamata yana kallonta ranshi abace yace "Ke" kallonshi tayi tana kuka mai taba zuciya, ahankali yakai hannunshi yakama hannayenta yadaura kan jacket din tawajajen kirjinta yace "hold tight" gyadamai kai tayi da kyar tana lumshe idanu hawaye na gangarawa yanabi ta gefen idanunta suna sauka a kunnuwanta, dan tsayawa yayi yana kallonta saikuma yakoma wajen kafanta ya tsugunna yashiga cirewa ahankali sabida zafin datakeji yaragu, sosai take kuka karshema sumewa tayi, ijiyewa gefe yayi sanan yakara daukan ruwan ya zuba kan kafan dayasa tafarka da kuka sabida zafin dataji, auduga yadauka zai mata dressing aka bude kofan aka shigo Aneesah ce agaba da Zeezee da Billy dawasu kawauensu sababbi guda biyu duk suka shigo gidan, tana mamaki waye mai mota irinta gidansu pake awaje ko some of friends dinta ne suka riga su zuwa. 💫 KYAWUNA JARABTA TA 💫 ✍️ M SHAKUR wa.me/+2347012181461 DUK WACCE TA KARANTA BATA BIYABA BAN YAFEBA, THIS BOOK IS 500 PAY INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK. EPISODE 5️⃣1️⃣ Wani kalan gajeren suma tayi tana nishi sama sama saikuma chan tabude idanunta batasan ya akayi ba ita datasan dasafe sukazo wajen nan gani tayi rana yasoma sauka komi najikinta ciwo yake mata kaman ba jikinta ba, kokarin tashi tayi amman taji takasa moving leg dinta hakan yasa da kyar ta karkata kanta takalli kafan dataji takasa motsi dashi jini tagani sosai akasan wajen kafin takalli kafan nata ganin kafan tayi kan wani katako da kusa biyu ke jikinshi kafanta na kanshi kusa biyu sun chaki kafanta sun nutse duka aciki, wani irin fashewa dawani mugun kuka tayi danji tayi tabama kanta tausayi wanan wani kalan rayuwa ne? Eh thought she will forever be happy awanan Abujan, who will save her anan tsakiyan dajin ya taimaka mata ko rarrafene tayi ta tafi gida, da kyar ta iya buda baki tadanyi ihu cikin kuka tace "ataimaka min dan Allah" ko motsi bataji sai kukan tsuntsaye danda alamu gidan gonan ma abandon one ne dan babu wani abin arziki aciki, sake dagokanta tayi kadan ta kwala ihu. "ataimaka min" wani kalan tsoro taji yana shiganta dan tasan a daji take tafashe da kuka sosai... Wasu gayune su hudu ke tafiya rikeda gorunan coke amman duk maihankali ya kalli goran ya kallesu yasan ba coke bane acikin goran ba idanunsu yay jajir suna tafiya suna layi, gasunan looking neat dan kana ganinsu kasan ba all this almajiran masu shaye shaye bane, kaman daga sama sukaji ihu ataimakenin Du'a duk tsayawa sukayi suna kallon kansu, daya daga cikinsu yace "kai Baaba na kwale ne koko da gaske ihun yarinya naji" atare sauran sukace "baka kwaleba Baaba muma munji" kalle kallen wajen suka shigayi suna layi dan abuge suke dukansu kafin su sakejin ihunta akaro nabuyi nan suka shiga neman saitin inda sukejin ihun. Jin tayi ihu tayi tayi amman babu alamun mutum yasa tashiga kalle kalle dan hakanan wayanta yafado mata arai, hango jakanta gefe tayi kayan ciki ma sun barbaje wayanta data hango agefe daban yaja tamika hannunta daya bala'in sage da kyar tana kokarin taba wayan baikai ba, fashewa da kuka tasakeyi sanan tasa duka karfinta taja jikinta da karfi wani irin fashewa tayida kuka takalli kafanta dake datse da katakon kutsan dake bulbulo bulbulo da jini sabida moving jikinta da tayi sanan tamikar da hannunta cikin ikon Allah hannun yakai wayan ahankali tadauki wayan sanan takoma ta kwanta flat, kasa daga wayan da kyau tayi ta kalla, saida tasake bata lokaci sanan tadaga hannunta tabude wayan da babu password tashiga keypad tana tunanin wazata kira watakeda number shi dan wanan sabon wayane, ijiye wayan tayi ahankali tasake fashewa da kuka dan hannunta yasake sakewa, ahankali tasake daga wayan wani zuciyan yabata data duba contact maybe tanada number dubawa tayi taga number daya kachal ne awajen da akai saving da emojin rings guda biyu, dialing number tayi takara a kunne tana runtse ido dan ita kadai tasan kalan azaban datakeji, wayan na gabda katsewa akai picking, cikin kuka sosai da muryanta dabaya fita sosai tace "Ya Asad kaine"? Batare daya amsa tambayanta ba strickly yace "what happen to your voice" wani irin ijiyan zuciya tasauke jinshine tace "Ya Asad bansan inda nakeba ina cikin daj......." daidai nan aka wani irin buga gate din da karan yasa ta firgice tasaki wayan takalli gate din dasauri, maza hudu tagani da gorunan coke a hannunsu idanunsu sunyi jajir suna layi suna kallonta dukansu suna bangaje juna suna dumfaro ta, daya daga cikinsu cikin muryan shaye shaye yace "kai Baaba mace yar shila nake gani haka akasa gasasshiya Allah ya ijiye mana ita mu kora da ita saman codeine dinan damukasha da harizona Baaba ko idanuna ne kemin gizo" dayan na gefensu dahar ya iso gabanta ne yaduka yana rike guiwanshi kaman wanda zaiyi ruku'u yana kallon Du'a cikin muryan maye yace "ehh wallahi Baaba kuma chakwai take" yakai hannunshi yashafa fuskarta dayaji fatar taushin tsiya kabarda hannunshi tayi tace "don't touch me, dan Allah kuciremin kusan nan daga kafana" karasowa sauran sukayi duk suka duka suna kallonta kaman basu taba ganin mace aduniya ba, yanda suke kallonta ga warin shaye shayen dasukeyi yasa tama fashe da kuka sosai. Tsaye yake yana karban wasu files dayasa akamai printing kaman ance yajuya yaga Asad nafitowa daga elevator daya bude ranshi a bala'in bace ga waya kare a kunnenshi, faduwa yaji gabanshi yayi ganin yay hanyar fita yasa yabishi da sauri yana kiranshi. "Asad Asad ina zaka, Asad" ko kulashi baiyiba yay wajen motanshi zai bude kenan Sharif yasha gabanshi yace "Asad bakaji ina maka magana bane I said what is wrong"? zare wayan yayi daga kunnenshi yamikama Sharif dasauri yakara wayan akunnenshi kukan Du'a yaji da muryan maza da su kansu awaya sunji yanda mazan suke abuge, dasauri yakalli Asad yace "ina Du'a taje data hadu da yan shaye shayen nan"? kasa magana yayi tsabagen yanda ranshi ke tafarfasa hakan yasa yace "kaga Asad zauna" yay maganan yana zaunar da shi sanan yakatse wayan yace "Du'a is using iPhone ko I can track her" wasu gurare yashiga a iPhone din Asad cikin 5min yace "got it let's go" zagayawa yayi yashiga dayan bangaren Asad yakunna motar yajata dawani irin mahaukacin gudu, Sharif yace maiyakai Du'a tsakiyan daji haka da babuma gidaje. Tsugunnawa duk sukayi akanta yanda kadai suke kallonta kaman sunga wata gasashiyar nama yasa Du'a take kuka sosai tace "dan Allah kuyakuri karku min komi" hamma daya daga cikinsu yayi yace "Baaaba nifa sonake nasa chaji awajen nan fa daman asama nake wlh" dasauri dayan yamike yana zare belt dinshi yace "ai wlh baka isaba nina farajin ihunta dan haka nizan fara saka chaji" na ukun ne yamike yace "kunga kuna harkan karanta dallah, daga ganin yar shilan nan bata tayi to miyene kuke wani rawan jiki, dukanmu zamusa chaji muyi gaba abinmu yan uwanta sazo su tsinceta ahaka bayan munsassaka chaji munyi full 100% mubarar da ita a achan bayan katangan gidan, amman yanzu shi Gwaska shizai fara tunda shi yafarajin ihunta yakuma ce mushigo gidan nan ba rushing mukadaine acikin dajin nan mukai hakuri kowa zai saka chajin" hakura sukayi shikuma wanda aka kira da Gwaskan kaman jira yake ya tsige belt ya yar yacire rigan jikinshi ya yar ya zare singileti shima ya yar sanan yazage zip din wando yaja wandon kasa, yarage dagashi sai dan gajeren wando, ihu Du'a tayi tana kuka sosai tana kokarin Jan jikinta baya kafanta na fito da jini, tsugunnawa Gwaskan yayi akanta yana murmushi sanan yakai hannunshi yawani finciki gyalen datai rolling dasaita yajawo da kanta sama sanan gyalen yacire kanta yakoma yabugi kasa kuma dayasa tai wani wahalallen kara. "durun uwa salatin arna! gashinta ne haka Gwaska" murmushi yayi yana bude goran coke din yadaga yakai baki yashanye sauran abin ciki duka sanan ya yarda goran yakai hannunshi zai taba kan Du'a tabude hannun tace "karka tabani" "Baaaba mai gardama ce wanan fa asamata karfi" "yanzu kuwa" yatashi yatsaya akanta yasata a osinshi sanan yakai hannunshi zaisa agaban riganta........ Kwanan shiga dajin Sharif yanunamai yace "we are going straight anan nake ganinta" shiga dajin Asad yayi da mahaukacin gudu amman ko mutum daya basu ganiba gadai alamu signal dinta suna gani amman basu alamun akwai mutane awajen nan ba gashi yamma tasomayi dan biyar saura, sunyi tafiya sosai suka fara hango wani old building mai gate dasauri Sharif yace "I think that's where she is"....... Kabarda hannunshi tasakeyi hakan yasa yace "Ke ni kike kabarwa da hannu" dasauri sauran sukace take hannun Baaba muga karshen tsiyanta, hannunta yakama yakai kasa yasa kafanshi yatake dayasa tai ihu sosai sanan yakai dayan ma kasa yatake sanan yakai hannunshi gaban riganta wajen biyun jikake kiiiiiiiiiiii ya barka rigan daidai an buga gate din anshigo dayasa dukansu suka juyo hardashi dake kan Du'a, Asad da Sharif ne suka shigo atare sunabin kowada kowa da kallo one by one kafin idanunshi su sauka kan Du'a dawani gardi ke tsaye kanta ya duka yana barka mata riga zuwa ciki ga black foamless bra na lace datasaka dayay parking boobs dinta da kyau tana wani irin kuka sabida yanda guy din yatake hannayenta, kallo daya Sharif yama side dinta baikaramata na biyu ba, Gwaskan dake tsaye kan Du'a ne ya kalle maza biyun dasukaci uban suit kaman masu aikin banki ne dasuka shigo gidan cikin muryan maye yace "kai dan gutsun uwarku kubar nan kuje kusami wani ginin kuje kuyi shaye shayen ku achan munriga mundau wanan" wani irin zuciya yadebi Asad wanda shi kanshi bayason yana irinta dan illata mutum yake kawai yaykan Gwaska dahar gyara tsayuwa yake akan Du'a yace "Au zoto abama hammata iska" Asad na zuwa baiyi wata wataba ya dunkule hannu yadaki kashin wuyanshi jikake kar wuyanshi ya karye, zai fada kan Du'a yawani dagashi da hannu daya yabuga abango sanan ya matsemai wuya kaman zai kasheshi, yana kakarin mutuwa idanuwanshi kaman zasu fito, ihu sauran sukayi zasuyi kan Asad dakecin uban Gwaska Sharif yataresu da nashi dukan yana barar dasu danko kadan babu karfi a jikinsu sabida yanda sukai shaye shaye kana dukansu suke barewa, idanda zakaga fuskan Asad zaka gudu makureshi sosai yayi cikin wani irin voice yace "how dare you touch my wife haaaaa!" kwalalo idanu Gwaska yayi kaman zai mutu amugun zuciye Asad yakama hannunshi yalumasu a idanunshi yace "saina tsiyayar da idanun daka kalleta dasu" sosai Gwaska yay ihu jin azaba a idanunshi, sanan Asad yawani irin gwara kanshi da bango ya barar dashi awajen assume ko motsi baiyi sanan yay inda Du'a take a kwance tana kuka takasa daga hannunta daya take akasa, jacket dinshi yacire dasauri yadagata yana kallonta yarufa mata akirjinta sanan yasake kwantar da ita ahankali, yanda yake abu zakasan amugun rude yake, gate yayi yafita da gudu booth dinshi yabude yadauko wani first aid kit dayake dashi yadawo ciki daidai Sharif yagama barar dasu yabiyo Asad din dagudu, kafanta da kusa kekai yabama Sharif yace "hold this kaga" karban kafan yayi da sauri yana kallon Du'a da idanunta ke kukkullewa kaman zata sume Asad shikuma yashiga bubbude komi na akwatin yana hadawa agefe sanan yadau wani ruwa yazuba akan ciwon, ihu tayi tana kokarin kwace kafan daga hannun Sharif dayaki saki, kafin yahada wani allura yamata sanan yakama katakon yatattaba jikin kafan kafin yafara pulling dinshi ahankali ihu tafara, taiwani juyi dayasa jacket din dayarufa mata yafadi tsayarda abinda yakeyi yayi da sauri yatashi yadau jacket din yasake rufamata yana kallonta ranshi abace yace "Ke" kallonshi tayi tana kuka mai taba zuciya, ahankali yakai hannunshi yakama hannayenta yadaura kan jacket din tawajajen kirjinta yace "hold tight" gyadamai kai tayi da kyar tana lumshe idanu hawaye na gangarawa yanabi ta gefen idanunta suna sauka a kunnuwanta, dan tsayawa yayi yana kallonta saikuma yakoma wajen kafanta ya tsugunna yashiga cirewa ahankali sabida zafin datakeji yaragu, sosai take kuka karshema sumewa tayi, ijiyewa gefe yayi sanan yakara daukan ruwan ya zuba kan kafan dayasa tafarka da kuka sabida zafin dataji, auduga yadauka zai mata dressing aka bude kofan aka shigo Aneesah ce agaba da Zeezee da Billy dawasu kawauensu sababbi guda biyu duk suka shigo gidan, tana mamaki waye mai mota irinta gidansu pake awaje ko some of friends dinta ne suka riga su zuwa. LITTAFIN NAN IS NOT A FREE BOOK, MAISON KARANTAWA DARI BIYAR NE 500, ZAKI TURO TA 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK SAIKI TUROMIN EVIDENCE OF PAYMENT TA WATSAPP NUMBER NA 07012181461. ZAKI IYA MAGANA DANI DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK wa.me/+2347012181461 WLH DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFIN NAN BATARE DATA BIYABA, MASU KARATU SATA DUK BAN YAFEMUKU BA DUNIYA WA LAHIRA, AND INA BAKU SHAWARAN KIYAYAN HAKKIN MUTUM. THANK YOU EPISODE 5️⃣2️⃣ Daga Sharif har Asad juyawa sukayi suka kalli gate din dasukaji anbude, hada idanu sukai da Aneesah dawasu yammata guda hudu, ganin Ya Asad da Ya Sharif dabata taba tunanin sune masu motan ba yasa jikin Aneesah yafara wani mahaukacin rawa sosai ganin Ya Asad da Ya Sharif akan Du'a datagani a kwance bata iya bude idanu da kyau ga jini yabata kafanta da hannun, ga jacket akan kirjinta, gawasu maza guda hudu datagani a sussume in various places, ga gorunan coke akasa wanda tasan da babusu, ahankali Sharif cikeda mamaki yace "Aneesah" sunanta da aka kira yasa Du'a tabude idanunta da kyar takalli gate din jin ankira Aneesah. "what are you doing here Aneesah who are this people"? kasa magana tayi sai rawa da bakinta yake tana kallon Ya Asad dako kai bai daga yakallesu tun bayan kallon farko daya musu najin anbude gate yacigaba da dressing din kafar Du'a abinshi, ganin yanda Aneesah tashiga trembling yasa ahankali da muryanta dabaya fita sosai cikin kuka ahankali tace "Ya Sharif nina kirata nace tazo" juyoda kai Sharif yayi yace "Ke kika kirata"? Gyadamai kai tayi ahankali, gama dressing din Asad yayi yakalli Sharif yace "I will go with the car zan kira akawo naka, call the police suzo su kwashi su" gyadamai kai Sharif yayi jikinshi yay sanyi dan no one needs to tell him Aneesah has something to do with all of this, idan Du'a ce takirata tayaya zatai locating this place dakoshi it took him time to track, badai son Asad yasa Aneesa did something as stupid as this ba. Tashi Asad yayi yadauki Du'a ahankali kankameshi tayi tana kuka ahankali dan ko Yaya aka tabata zafi takeji, ahankali yake tafiyada ita dasauri Aneesah da kawayenta suka matsa gefe takasa kallon Ya Asad, shima ko kallon inda take baiyiba yawuce yafita, sata abayan mota yayi ahankali yana kallonta kwantar da ita yayi sanan yarufe motan yadawo gaba yashiga yaja motan, saida Sharif ya tabbatar da yatafi sanan yakira police kafin yatashi yataho inda Aneesah ke tsaye kanta akasa har lokacin jikinta yakasa daina rawa yace "tell me u have nothing to do with this Aneesah" kasa dagokai takalleshi ma tayi, yanda jikinta kerawa haka na kawayenta ma suka shiga rawa, Billy datafi kowa tsoro barinma dataji ankira police yasa tace "Aneesah Brother wallahi we don't know this guys" kallonta Sharif yayi strictly yace "just tell me what happened" nan takoromai bayani tundaga kan plan din da sukayi a group na yanda zasuci uban Du'a, sanan takarashe da fizge wayan Zeezee tabude tanunama Sharif video da Zeezee tayi tana ihu tana kara tunzura Aneesah tana kiban Du'a kaman yarta tana kuka tace "wlh ko yatsunmu daya baitaba Du'a ba, Aneesah tai komi mu kawai yan rakiyane dakuma hyping" karban video yayi yana kallo kasama jure kallon video yayi yatura wayan aljihu yashiga dukan ta da kafa da hannu tana kuka sosai polisawan dasuka zone suka rikeshi sanan yabarta tafiya da guys din akayi sanan yasata a motan da Asad ya aikomai dashi suka wuce batare daya bada wayan Zeezee ba. Awani private Asibiti ya tsaya yana parking yafito daga mota yashiga ciki ma'aikatan asibitin sai gaidashi suke, direct pharmacy dinsu yaje yan phamarcy na gaidashi abubuwa yadinga kwasa batare daya amsasu ba yacika wani babban leda sanan yafito mota yashiga yaja motan da mugun gudu, yana zuwa anguwan su direct gidan Hajiya yawuce ana budemai gate yaja motan ciki, sanan yafito tabude baya, Du'a da idanunta a kulle yakai hannunshi yataba jin jikinta yay sanyi yasa yay sauri yadauketa yakalli security yace "bring one big leather from the car" sanan yay cikin gidan da ita, sallama yayi yabude kofan, Grandma na zaune kan kujera ganin Du'a a hannun Asad da fuska yay subu subu ga kayanta yay datti jacket din Asad ne akan kirjinta kafanta jini kasan riganta dukya baci da jini yasa tawani mike tsaye arude tace "innalillahi wa innailaihi raji'un, maiya sami Du'a" sama yayi Grandma tabishi da sauri dakinta yabude yashiga kwantar da ita akan gado yayi, sallama sukaji daga kasa na Dad da Ammi dasauri Grandma data rude tafito ganin su Dad ne da Ammi, da Rahima, Mariya da Anty Turai yasa abin yabata mamaki, Dad da jikinshi yafi kowana rawa yace "what happen maiya sami Du'a Hajiya yanzun nan Sharif yakiramu yace dukanmu muzo gidanki something happen to Du'a shima yakusan karasowa tareda Aneesa" ahankali Hajiya tace "nima bansani ba yanzu Asad ya shigo da ita asume" dasauri sukai dakinta da Asad ke kokarin fixing mata drip, zaro idanu Mariya tayi tana salati aranta me Aneesah tama Du'a haka, cemata tayi magana fa kawai zata mata tabata tsoro what happened to her like this, tsayawa duk sukayi kowama yakasa magana ganin yanda Asad ke komi dasauri sauri, yana saka allurai a drip din, saida yagama tass sanan yadawo kafanta dasuka a yasha bandeji budewa yayi yana dressing duk suka tsaya suna kallonshi sanan yakama hannunta yamata alluran tetanus kafin yasa stethoscope yana kokarin dubata Sharif yay sallama yashigo yana rikeda hannun Aneesah da idanunta sukai jajir, ganin yanda suka cika dakin yasa Dad yace "duk kumu fito falo, Asad muna jiranka" fita duk sukayi harda Grandma suna kallon Asad zare stethoscope din yayi jin heartbeat nata yay stabilizing sanan yafito ahankali ya tsaya bakin kofan dakin yay folding hannunshi a kirji yana kallon Aneesah dake kuka idanunta akasa, ahankali Dad yace "Asad Sharif maiya sami Du'a? kuke tareda ita a office" ahankali Asad yace "she never came to the office yau, katambayeta what happen" yay maganan yana kallon Aneesah dakowa yajuya yana kallo, Anty Turai tace "ke what happen ake cewa atambayeki" hawaye tashare ahankali kanta nakasa tace "Mum inason Ya Asad ne" shiru kakeji adakin sanan ahankali tace "and Du'a is my best friend ita kadai nafadamawa shine ta auri Ya Asad, shine......" tashiga koro bayani tundaga kan yanda suka cireta a group harzuwa yau tace "Dad, Ammi, Mum wlh wlh bansan guys dinba bani nasasu ba, the plan was kawai muje muyi dambe taji tsoro tarabu da Ya Asad" ahankali Sharif yaciro wayan kawarta Zeezee yamikama Dad yace "Dad look" karba Dad yayi ranshi yay masifan baci, Du'a dayake so Aneesa ke jibga haka shida baya dukan yaranshi koda wasa baisan lokacin daya yarda wayan yawani jawo Aneesah yakifa mata mari ba yace "is this the way I train you Aneesah to be this wicked? All what our family knows is love not hatred Aneesah kinsan mekikayi kuwa eh inda kin kashe yarinyar nan dame zaki fadima iyayenta" Dad yakara kaimata mari zuciyanshi na tafarfasa dan abin yamai ciwo ainun, ganin zai sake kaimata mari yasa Grandma taja Aneesah taboye abayanta tace "agabana saikaita dukan yarinya bakada kunya ne, Aneesah yarinyace children now a days do crazy things for love eh, besides her intention was even childish all abinda take dashi aranta shine suyi fada kawai ayi dambe which is very very normal and okay, batayi agida bane sabida za'a raba fadan dawuri saisa takaita where she feels zasuyi fadan and settle everthing yisu yisu, please nobody should touch this girl again, Sharif Asad, no one should lay a finger akan Aneesah, haba jibi idanun yarinya" kankameta sosai Aneesha tayi tana kuka sosai tace "Hajiya I am so sorry wlh bazan karaba, wlh bazan karaba dan Allah kuyakuri" ganin yanda yarinyar ke kuka harwani ijiyan zuciya take yasa Anty Turai taji takai wuya dan marin da Dad yamata yamata ciwo matuka, hannun Aneesah taja tace "ke wuce muje tattara yinamu yinamu mubar musu gidan nan, sabida yana kula dake yana biya miki school fees a private university shine zai wulakanta ki haka" cikin wani azababben fushi dakowa yadade bakiga Dad dashi ba yace "wlh wlh Turai kikaja yarinyar nan kikabar wajen nan saina mugun saba miki karyan rashin kunya kike, fitsararra saisa babu namijin dake iya zaman aure dake" cikin fushi sosai jin cin fuskan da Dad yamata Turai tajuyo takalli yayan nata tanunamai dakin da Du'a take ciki tace "nikake gayama magana Yaya? Eh? condition din da yarinyar chan keciki yanzu y'ata ce tasata aciki? Ba ita bace and we all no that, abinda Aneesa tayi was silly abu da yara mata duka sun sabayi, duk maganan Du'a kuke no one is talking about Aneesah, bayan dukkunsan soyayyan danku wanan ja'irin yaro yasa taje tana fada da Du'a, ita maisa bazaka aura mata Asad dinba eh kabar gida kaje waje kana aurawa danka yarinyar dabatada gata agidan ubanta, wanan shi ake kira da bishiyan giginya yahana na gida inuwa yabama nawaje, sonkai kawai sanan dannai magana kake gayamin irin halin yasa nakasa zaman gidan miji" cikin fushi Dad yadaga hannu zai kwasama Turai mari dasauri Ammi tarike mai hannu tace "Alhaji calm down dan Allah children are here" cikin fushi Turai tace "barshi ya maren mana, I no blame him daman ance yarinyar mayya ce, so anything can happen gashinan daga aurama Asad ita gidanmu ya haukace, gidanmu that has been peaceful for years yarinya rana tsaka tashigo tana neman daburta komi, wlh bakuga komiba baku dai Allah yazuba muku kwashe kwashe ba kucigaba, yarinyar da agidansu neman kai akeda ita amman kuka jida" ahankali Ammi takama hannun Anty Turai ganin maganganunta are hurtful kuma ga Hajiya awajen tace "Anty Turai dan Allah kiyi shiru this whole thing baikai ga haka ba" tura Ammi tayi baya cikin bakar masifa tace "dalla munafuka kyaleni" baya Ammi tayi zata fadi dasauri Dad da Sharif suka tareta aiko Dad nadagowa baiyi wata wataba yadauketa da lafiyayyen mari zaikai mata na biyu sukaji muryan Du'a kaman daga sama cikin yar siririyan muryan nan nata tace "Baba". Assalamu Alaykum, inaso mu gina al'umma masu tsoron Allah da tsoron hakkin dan uwanshi musulmi, I was very kind and generous nayi pages talatin da daya (31) pages awanan littafin as free, dan Allah kudubi Allah badan niba badan halina ba karku karanta idan baki biya kin shiga group ba, dan idan kikai gaskiya Allah zai bimin hakkina. Kudin karatun this novel is 500 kacal, pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting. you can chat me up directly a watsapp by clicking on this link wa.me/+2347012181461 ✍️ M SHAKUR EPISODE 5️⃣3️⃣ Dasauri Asad yajuyo yakalleta tana tsaye abayanshi dafe da bango ta cisge ruwan dayake kara mata idanunta sunyi jajir sun kumbura tsabagen kuka tana kallonsu, wani kalan mugun kallo yamata, murya ciki ciki ta yanda su Dad bajinshi zasuyiba yace "maisa kika sauko" ahankali kanta na kasa tace "I am sorry" dasauri Ammi ta taho wajen tana kallonta, hannunta tarike tana kallon fuskanta tace "maisa kika tashi Du'a keda akema treatment" murya chan kasa tace "Ammi dan Allah kaini falo" yanda fuskanta kadai yayi yasa Ammi bata musa ba, rikota tayi tafito da ita falo ta zaunarda ita akan kujera, da kyar ta zauna tana cije lips sabida yanda kafan kemata zafi ahankali sanan tadaga kanta ta kalli Dad kafin ahankali takalli Grandma dakowa na falon dake kallonta cikin wani irin murya dake taba zuciya tace "dan Allah kuyakuri kudena fada sabida ni, kuyafemin, Aneesa kema kiyakuri" sanan ahankali takalli Grandma idanunta suncika da kwalla sosai tace "Grandma inaso zan koma kano chan gidan mu!" kowa kallonta yake cikeda mamaki barinma Dad da idanunshi ke neman fadi kasa jin yanda tace zata koma gida, hawayen dasuke zubomata tashare da bayan hannu tace "nariga nabata zaman lafiyan gidanmu, I've caused alot of trouble banson nazo nan kuma nahaddasa fada a family ku, I don't wanna cause any trouble, gwara nakoma chan gidan ubana inda ansaba fadan dama sabida ni, maybe after all abinda mutane kecewa akaina is true ni bad luck ce sanan ni mayya ce, ni kaina nasoma yarda da hakan, gashinan daga zuwa na Abuja anata fada sabida ni which nasan da baku tabayi ba, Grandma dina na sonku sosai bansan sabida ni mu'amalanku dakuka gina da dadewa tabaci, inaso Ya Asad yarabudani, yasakeni nakoma kano suyi aure da Aneesah kowa yahuta" shiru tayi awaje saita daura duka hannayenta biyu akan fuskanta tafashe dawani irin kuka mai sosoran duk wani mai imani, cikin kukan tace "Mami na ita kanta tace tunda tahaifeni bata kara samin kwanciyan hankaliba balle ku, ni kaina bansan mecece niba, I don't know myself, nafita daban dakowa danasani, nafita daban da iyayena da yan uwana, gabaki dayan danginmu banyi kama da kowaba, ko'ina naje ayita kallona ana cewa inada kyau, kyan dabanaso, kyan dana tsana, KYAWUNA shine JARABTA TA, KYAWUNA yazame mini JARABTA, wlh kaman na mutu kowa yahuta nakeji, nobody loves me, nazama musiba aduk inda nasa kafa, Ya Nana da Ya Hawwa duk basa sona, sabida kyan danake dashi yasa suna boyemin komi na rayuwansu da samarinsu sabida suna tunanin suna ganina zasuce ni sukeso, wanan ba KYAWUNA JARABTA TA bane?? I just want to die nakoma wajen ubangijin daya halliceni and rest, I want peace, I need peace, and from look of things peace can never be mine a duniyan nan saidai idan nakoma ga Allah kowama yahuta" dasauri Ammi da idanunta sukai jajir tazo gaban Du'a kneeling tayi ahankali takama hannun Du'a dakekan fuskarta tana maganan tana kuka tasaukar dasu kasa, kuka harda majina, ahankali Ammi takakalo wani sad murmushi sanan tabude baki zatai magana saikawai taji takasa rike kukan dayazo mata fashewa sosai tayi da kuka agaban kowa na falon, maganganun Du'a sun sosamata rai, sun tabata, Du'a don't deserve this at all, yarinyar tabata tausayi matuka bana wasaba, ahankali Asad yajuya yay stairs yasauka yabar gidan abinshi, shi kanshi Dad waje yanema yazauna jikinshi yay la'asar sosai ya bala'in ji tausayin Du'a samada koda yaushe, Sharif ma idanunshi sunyi bala'in ja sabida tausayinta, itako Rahima share hawayen daya zubomata tadinga yi dan she couldn't hold it, Du'a tabata tausayi ainun she was just imagining kanta a situation din Du'a batai tunanin she can even handle kanta kaman yanda Du'a tayiba, Mariya ma idanunta sukai jajir tai bala'in nadaman all she said to Du'a a chat da yanda ta shareta yau dan yarinyar nan don't deserve any form na mistreatment, Du'a have been through he'll da all she deserves right now is love, jitayi she hates herself for what she did to her, Aneesa ma dake jikin Mamanta itama jikinta yay sanyi kaman kankara, Grandma kuma murmushi tayi tasami gu tazauna ahankali, a yau takara yarda iyayen Du'a sune suka fara kashe yarinyar nan suka mata illa before anyone, sabida ko kadan basu jata ajikiba sun sota sun nuna mata karta sake tadauki KYAWUNA amatsayin JARABTAN TA rather tadauki KYAWUNTA amatsayin BAIWANTA, baiwan da Allah yamata, amman duk basuyi hakan ba sunsa maganganu da kalaman da mutane suke fadi mata na mayya, aljana, bad luck sun gino sun zauna aranta, sun kulle yarinya agida batare da sunyi connecting da itaba sun nunamata soyayya ba, at least koda sukai grounding nata dasun jata ajiki sun sota bawai su ware ta ba none of this would have happened, wanan wasu kalan iyayene???? To think daga jikinta Mami tafito abin nabata mamaki dan inda ita tahaifi yarinya irin Du'a bazata taba mata abinda Mami tama Du'a ba. Ammi tadade tana kuka tareda Du'a takasa lallashinta kuma babu wanda yay attempting lallashin su sanan ta lallashi kanta da kyar tadago takalli Du'a kafin ahankali takai hannunta kan fuskarta tai cupping face nata tace "listen Du'a idan kowa na duniyan nan bayasonki sun tsaneki I want u to remember this ni ina sonki sama da danda nahaifa Du'a, and koyau kika wayi gari kikaga bakida kowa Du'a kinada ni, I've loved you kafin nama ganki ask Hajiya tagayamiki, dana ganki I even loved u more because all I see in was a special, beautiful, intelligent, talented and innocent young lady, and u are not a bad luck Du'a, duk wanda sukace miki ke bad luck ce karya suke, infact u are a gift a family ku saisa Allah ya yiki daban sabida yanuna musu ke gift ce, and u are special saisa kyawunki, karismanki natsuwanki daban, saisa kikeda shiga ran mutane nan da nan aji ana sonki cus everything about you Du'a is unique, they see that as bad luck while ni da duk wasu masu ilimi da hankali da tunani see it as gift! which makes u a very special child Du'a" Ammi tai shiru tana kallonta ganin Du'a tadena kuka tana kallon Ammi ahankali da idanunta dasukai jajir, murya chan kasa tace "u were never and will never be a bad luck Du'a! Fadan dakikaga babanku yayi da kanwanshi is just something that was bound to happen bakece kikasa akai fadan ba, Du'a I want you to love yourself! Kitso kanki sama da komi arayuwan nan, value yourself, sabida baki valuing kanki saisa kowa ke takaki yanda yaso, Value yourself, carry yourself with dignity and self worth, stop blaming yours for anything dake faruwa a inda kike, danba laifinki bane, stand up for yourself, duk wanda yakiraki bad luck ki gayamai u are not a bad luck you are a gem, and start living ur life, dat life dabaki same shi kinyi ba leave your life now and enjoy all the luxuries life has offered u, kinriga kinbar gidanku keda zuwa saida izinin mijinki, you are married yanzu, forget ur past and enjoy this present and be happy Du'a, I want to announce this to you and everyone here amatsayina na mahaifiyar Asad nasaka ranan bikinku wata daya, za'a biki akaiki da kinki, maganan Asad yarabu dake karki kara yinshi, inaso ki manta da komi kiso kanki kinji" gyadamai Ammi kai tai ahankali fuskanta nakan hannun Ammi, Ammi takai hannunta tana share fuskanta sanan tajuyo da kanta takalli Aneesah, ahankali Aneesa tazo wajen hawayenta tashare takalli Du'a cikin wani sabon kukan dayazo mata tace "I am so sorry Du'a dan Allah kiyakuri, and wlh nahakura da Ya Asad din kiyafemin please Du'a" murmushi Du'a tayi hawaye na zubomata tace "Aneesah na yafemiki" zuwa kawai Rahima tayi tama kasa magana rungume Du'a tayi tsam ajikinta, tadade ahaka sanan tasaketa tace "from today I will be ur sister, bakaman su Hawwa da Nanan kuba, I will be a real sister to u Du'a and ur mentor, no one will bully u again, I promise you that, kinason hakan"? gyadamata kai Du'a tayi tana murmushin kuka ahankali, zuwa Mariya tayi itama ta tsugunna gefen Rahima tana kama kunnenta duka biyun tace "Du'a I am sorry, dan Allah kiyafemin" murmushi Du'a tayi tana kuka dan she can't believe itace mutane ke tsugunnawa agabanta haka suna rokon yafiyanta, saikawai ta rungume Mariya dan tama kasa magana sabida kuka, zuwa Sharif yayi wajen shima, ga mamakinta shima tsugunnawa yayi kusada Mariya yana kallon Du'a hakan yasa tasaki Mariya ahankali, murmushi yamata idanunshi sunyi ja shima yace "tunda kinsami sisters har uku, is there any space for big brother"? Wanan karan wani irin fashewa tayida kuka, hararanta yayi yace "okay Du'a na lura village people dinki naso susakani kuka agaban yara ko"? Yay maganan yana goge hawayen daya zubomai dasauri da bayan hannu dan baiso yay kuka, rungumeshi ahankali Rahima tayi dan tasan what's going on azuciyanshi, Mariya itama rungumeshi tayi, hakan yasa Aneesah itama ta rungumeshi, ahankali Du'a ta rungume su, duk sukahau kuka, wanan karan duk dauriyan Grandma saida tajuyarda kanta gefe ta share hawaye dasauri, all she sees right now is family Allah yama Du'a kyautan family da inda ayanzu zata fadi tamutu burinta yacika dan yanzu Du'a will know what peace and love is, Alhamdulillah nothing last forever, ance bayan wuya sai dadi, Ayar Allah ta tabbata wanda yace WAMAI YATAWAKKAL ALALLAHI FAHUWA HASBUK, wato duk wanda yadogara ga Allah to Allah ya isar masa, Du'a tai hakuri tai imani, she has been quiet, ta wahala but hakan baida takaucema Allah ba, gashinan Allah yasaka mata da wayanda sunmafi family nata. Sun dade ahaka sanan suka saki juna, murmushi duk sukayi kowa looking so emotional and very happy at the same time. TUNATARWA GA IYAYE PLEASE IYAYE MATA DA MAZA, DAN KUNHAIFI YARO MAI NAKASU KO YARON DAYAFITA DABAN AYARANKI, KIJASHI KI SASHI AJIKI, DON'T TREAT UR KIDS YANDA IYAYEN DU'A SUKAYI, I HOPE U ALL SEE THE LESSON DA SAKON DANA ISAR ACIKIN WANAN LITTAFIN ❤️ 5️⃣4️⃣ LITTAFIN NAN IS NOT A FREE BOOK, MAISON KARANTAWA DARI BIYAR NE 500, ZAKI TURO TA 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK SAIKI TUROMIN EVIDENCE OF PAYMENT TA WATSAPP NUMBER NA 07012181461. ZAKI IYA MAGANA DANI DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK wa.me/+2347012181461 WLH DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFIN NAN BATARE DATA BIYABA, MASU KARATU SATA DUK BAN YAFEMUKU BA DUNIYA WA LAHIRA, AND INA BAKU SHAWARAN KIYAYAN HAKKIN MUTUM. THANK YOU Tashi Dad yayi da jikinshi ya bala'in yin sanyi wani son Du'a nakara shiganshi yace "bari naje kuga inada meeting" sosai yake tafiya yake tunani baitaba shiga tsaka mai wuya arayuwanshi irin na wanan lokacin ba, how is he gonna settle this situation, yabar Asad ayi bikin ne koko yasan yanda zaiyi ya kashe auren, but yakashe auren yanada chance on Du'a kuwa? Family shi dahar Hajiya zasu tsaneshi kuma duk yanda zasuyi saisunyi sun kaita nesada shi ta yanda bazai kara ganinta ba, karyay acting like a fool, instead yayi abinda yasan will benefit him, dan haka he should calm down and get Du'a in their game batare da kowa ya lura ba, hardan sa idon dannashi. motanshi yashige yatafi. Kallon Grandma Ammi tayi tace "bari naje Hajiya" gyadamata kai tayi, Anty Turai ma ta tashi takalli su Rahima tace "kutashi mutafi" tashi duk sukayi suna murmushi, waving hannu suka mata sanan suka wuce, Sharif yakalleta yace "kina bukatan anything"? Girgizamai kai tayi hakan yasa yace "bari naje gida" wucewa yayi hakan yasa ahankali Grandma tazo wajen tana kallonta ijiyan zuciya tasauke sanan taduka ahankali tadagata, da taimakonta takaita dakinta bayi suka wuce, bata mata wanka ma amman saida tagoge mata jikinta tass sanan suka fito bayan tamata alwala tadauko wani gajeren rigan bacci cotton ne iya cinya tasamata sanan tasamata hijabi tazauna da ita bakin gado tace "yi salla bari naje nakawo miki abinci" sauka Grandma tayi kasa, su Razika tagani a dinning sunyi wani iri tasan sunji komi, murmushi tamusu tace "kuje ku ganta" kaman jira suke dasauri sukai sama Grandma tai murmushi dan yau burinta yacika she's so happy hada mata simple abinci tayi spaghetti sai farfesun tantabaran da aka mata na kayan mata sanan tadawo sama su Razika tagani tareda ita suna ganinta duk suka tashi zasu fita taresu tayi tace "ina zaku kudawo" tai maganan tana kallon Du'a datai dan murmushi kana ganinta kasan zazzabi ke cinta, zama Grandma tayi gefen gadon tace "zokici abinci saiki bacci" gyadamata kai tayi, Grandma takai taliyan bakinta just two spoons tayi ta juyarda fuska tanaji kaman zatai amai tace "Grandma amai zanyi banso" cikeda damuwa Grandma tace "to dan Allah kidan kara babu abinci acikin ki, konayo miki tea?" dasauri ta gyadama Grandma kai ahankali, tashi Razika tayi dasauri tace "bari nahado mata tea Hajiya" murmushi Grandma tayi tace "tom Razika" dan kishingida Du'a tayi da jikin gadon kafin kaceme bacci yay awon gaba da ita, ko 3min Razika batayiba tadawo rikeda mug din tea, karba Grandma tayi Razika na kallon fuskarta tace "ai tamayi bacci" ijiye tea Grandma tayi kan side drawer tace "ai yanzu zan tadata tasha" dasauri Razika tace "please Grandma karki tadata anjima ta farka zatasha" shiru Grandma tayi tana kallonta zatai magana sukaji anyi knocking kofar dakin, dasauri duk suka dagakai dan Razika taba kofan kadan abude dan bata gama rufewa ba ganin Asad ne tsaye yajuya musu baya yana daddanna wayanshi ya chanza kaya zuwa 3quater wando daya tsayamai a guiwa brown sai wani clean white t-shirt yana zuba uban kamshi yasa Grandma ta tashi takalli su Razika dahar sun tashi tace "kumuje Shema'u, ga mijinta nan" fitowa sukayi daga dakin, su Razika suka gaidashi suka wuce kasa, fitowa Grandma tayi takalleshi tace "Asad kazo, wlh inata fama da ita takicin abinci, kuma koda safe batai breakfast na kwarai ba tafita, Du'a batason abinci yanzu ma bacci tayi bataci abincin ba, anmata tea tai bacci, kuma ruwan data tsige ni bansan yanda ake maidawa ba akwai zazzabi ajikinta" gyadamai Grandma kai yayi yana wani dauke kai, Grandma tace "bari naje nai salla banyi salla ba wlh sabida yarinyar nan" Tai maganan tana wucewa, saida yaga tabude kofa tashiga dakinta sanan yabude kofan dakin ahankali yashiga yamaida kofan yarufe sanan yajuyo yana kallonta yanda take bacci atakure ta jingina bayanta da bangon gado, ga tea dinta da aka rufe ga spaghetti da farfesu duk anrufe, ahankali yatako yakaraso zuwa cikin dakin, gaban gadon ya tsaya yana duba drip din, sanan yaduka yakama hannunta ahankali ya mayarmata dashi ganin baya tafiya, yasa yajuya yabude ledan yadauko syringe yabude yazuko ruwan drip din sanan ya tsugunna yakama hannunta yasa syringe din yana flushing, yatsine fuska tayi tareda juyarda kanta jin zafi hakan yasa ya tsaya ahankali yana kallon face dinta, ganin tadena motsi yasa yacigaba sake yatsine fuska tayi tana juyarda kanta saikuma tabude idanunta ahankali daidai yana karasawa sanan yamaida yatashi, ahankali takalleshi ganin shine yasa tadan dauke kanta tanajin wani irin mugun bacci, zama yayi ahankali kusada ita sanan yadauki mug na tea yana juyawa da spoon kafin yadebo tea yakai bakinshi jin babu zafi yasa ya ijiye yajuyo yakalleta yanda take kallon gefe, ahankali yakai hannunshi kan shoulder dinta dasauri tajuyo da kanta ta kallai, hada idanu sukayi yace "come and have dinner" kasa magana tayi sata ajikinshi yayi ta side gabaki dayan hannunshi daya nata bayanta yadaura akan kafadanshi yayi kaman cuddling nata ta side sanan ya juyar da kanshi yadauki mug na tea yakawo wajen fuskanta yakai bakinta yana kallon fuskanta ahankali yace "drink" kurban tayi kadan sanan ta ture kanta tana yatsine fuska sosai dan bakinta baya mata dadi ahankali yana kallonta still yace "what"? murya chan kasa kaman wacce ke shirin yin kuka tace "banaso, nakoshi" yana kallonta har lokacin yace " have u had ur breakfast"? girgizamai kai tayi yace "lunch?" Girgizamai kai tayi, hakan yasa murya chan kasa yace "you have to finish this tea" yakai mug din bakinta ahankali tai sipping sanan tacire baki tana yamutse fuska, cikin wani kalan kakkausar murya yace "Ke" dasauri takalleshi gabanta nafaduwa, batasan lokacin datakai bakinta mug dinba tashiga shan tea dasauri sauri saida takusan shanyewa taji amai yazo mata yunkurin aman datayi yasa yacire cup din daga bakinta dasauri yana bubbuga bayanta, ijiye cup din yayi dasauri sanan yakamo kanta zuwa kirjinshi ya kwantar yana shafa bayanta sosai takejin aman yana tasomata amman kamshin turarenshi dataji yasa taji tana wani irin calming down, dakuma yanda yake shafamata baya, wani irin lumshe idanu tayi tana sauke ijiyan zuciya takara yin lamp dakanta akirjin dataji yamafi pillow dinta taushi dakuma cika gashi so huge, ganin she's calm takara shigewa jikinshi ta chusa hancinta a kirjinshi yasa ya gyara kafafunshi yay spreading nasu akan gadon yadagata yasata a in between legs din nashi kanta na kirjinshi which is very good dan baibari ta kwanta immediately bayan taci abinci ba tana zaune ne, kafafunta zuwa cinyoyinta dake waje yabi da kallo ga sanyin AC adakin ahankali yasa Yatsun kafanshi yaja bargo yamika hannunshi yay spreading ya rufa musu sanan yakoma ya jingina da gadon yana kallon fuskarta ganin idanunta a lumshe suke, hannunta da drip kebi yakalla ganin position dinshi is perfect yasa ahankali yakara kankameta a kirjinshi yakai hannunshi daya yasa acikin kanta yana yamutsa kitson yana mata wani irin scratjng scalp da massaging kanta dayasa tasaki wani irin ijiyan zuciya wani bacci mai bala'in dadi na dibanta kafin yaji tasaki dan nauyinta daba na kirki ba ajikinshi tai bacci. Ajiyan zuciya yasauke shima ahankali yana kara kankameta a jikinshi wanda baijin yataba helding nata this close and tight ba sai yau, gawani cool kamshi da jikinta keyi dat he so much love, she feels tender a hannunshi, little and innocent like a little girl that needs his help, yana rikeda ita ahaka wayanshi yaji yana kara, dasauri yadauki wayan gudun karta tashi ganin Ammi ne. "Asad nazo side dinka bakanan kana ina"? ahankali yace "ahhhhmm" daga tadayan bangaren Ammi tace"kaje duba matarka ne, okay kazo ina dakinka ina jiranka" bata jira amsanshi ba takatse wayan. Ahankali ya ijiye wayan yana kallon fuskar Du'a dake jikinshi, dan yatsine fuska yayi kaman wanda baiso yaje, ahankali yana rikeda ita yajuya ya kwantar da ita gently, sanan yasaketa ahankali yatashi yana kallonta, idanunshi ne suka sauka akan boobs dinta dayake nan kaman sunmafi girma idan batasaka bra ba compare to idan tasaka, dan juyarda kanshi yayi da sauri saikuma yasake juyoda kanshi yakallesu ta cikin rigan, kaman wani abuna janshi ahankali yaduka kaman wanda zaiyi ruku'un salla yana kallonsu sanan gently yakai hannunshi dahar rawa rawa yakeyi yadaura akan left boob din tasaman riga, wani kalan shock jikinshi yadauka baisan lokacin daya za,,,me hannunshi ba yakoma ba dasauri yajuya yafita ko tunawa yadauki wayanshi baiyiba. I5️⃣5️⃣ Baazan gaji da fadi ba duk wacce tacimin hakkina ban yafeba, a word is enough for the wise🤷‍♀️ THIS NOVEL IS 500 PAY INTO 3107021073 AISHA Muhammad first bank. chat me up directly by clicking on this link wa.me/+2347012181461 Ahankali yaturo kofan flat dinsu ya shiga, Ammin shi yagani zaune akan kujeran falonsu tareda Sharif dake zaune agabanta akasa yadaura kanshi akan cinyanta tanamai head massage suna hira, ganinshi yasa tai murmushi tanunamai kujeran dake facing nata tace "zoka zauna anan Son" maida kofan yayi yakaraso ciki yazauna ahankali, cire hannunta tayi dagakan Sharif din tadan bugi bayanshi alamun yatashi hakan yasa yatashi yazauna agefenta, dan gyaran murya Ammi tayi tana kallonshi, anatse tace "Asad bazan tsaya boye boye dakai ba znine mahaifiyar ka kai d'ana ne, the truth is banso kuma bazan taba bari aurenka da Du'a ya rabu ba" kallonta yake Asad ahankali hakan yasa gently tace "yes Asad nasan nashigi rayuwanka da yawa dankai aure baya gabanka, but son u are 33 yanzu going to 34, sai when zakai aure? Eh Asad, abu daya yakawoni nan side dinku, nazone musamman nagayamaka idan akwai yan gyare gyaren daza'ayi agidanka kafadamin nasa afarayi nan da 1 month that's sati hudu masu zuwa kenan za'a taron bikinku akai Du'a gidanka kaima katattara kabarmin gidana kaji" tunda take maganan yake kallonta harta gama yanayin jikinshi ko fuskanshi bai chanza ba, Asad is just somehow da saiyazo kagane mood nashi ne zaka gane, ganin yanda yayi yasa jikin Ammi yasoma sanyi but bataso takaraya, ahankali tamike tsaye taje gabanshi ta tsaya, saikuma yaja stool din gefen kujeran tazauna a gabanshi hannunshi guda biyun ta kalla sanan takalli fuskanshi ahankali tace "Asad nasan koda bakason Du'a kanajin tausayin yarinyar nan dan I see it in your eyes, bazaka iya taimako ba? Du'a yarinya ce mai bala'in hankali da natsuwa, barta dai da rashin wayo, tsoro da saurin kuka shima duk sabida yanda ta tasone nan gaba duk zata watsa dasu ta kile, Du'a yarinya ce da I assure you zakaji dadin zama da ita, d only problem da nasan Du'a nadashi is rashin iya girki which yanzu tafara koya, shima rashin iyawan sabida agidansu ko kasa ba'a bari ta sauko ne anyi banning nata daga shiga kitchen, Asad do this for me, for ur Ammi dakake so kaji" ganin yaki magana yasa ahankali Sharif yace "Asad" dagokai yayi yakalli Sharif saikuma ahankali yacire idanun daga kanshi yakalli Ammi ajiyan zuciya yasauke yace "Shikenan Ammi I will start with prep" tsabagen murna Ammi batasan lokacin datai kissing kumatunshi ba, Sharif yace "I will handle IV, dinner da....." yatsine fuska Asad yayi ahankali yakalli Ammi yace "Ammi tell him banason hayaniya please just low key taro zakuyi awatse I am not gonna be present in anything koda kun gayyaceni" Sharif zaiyi Magana Ammi tadaga mishi hannu alamun yayi shiru subishi ahaka, dasauri tace "shikenan Asad kome kakeso haka za'ayi, yanzu zan fara hada akwati, zan shiga Dubai nama gayama Baban ku inaso naje nai 3days nayi siye siyen kayan akwatin ta" tabe baki yayi yana taba aljihu trying yaciro wayanshi dan in ana surutu dabaya burgeshi waya kadai yake tabawa yaji dadi, jin bawayan yasa yadanja gajeren tsaki ahankali tuna yabarshi agidan, ba yanda ya iya haka yahakura yana jinsu suna shirye shirye har suka gama baikara kulasu ba. Wuraren 3 ta farka daga bacci, bin dakin tayida kallo dan ba'a kashemata wutaba, batajin any ciwo banda kafanta da kusa ya shiga dake mata zafi danshine ma yatadata daga baccin, tashi tayi ahankali tazauna abakin gado tana kalle kalle, saikuma takalli kafan dake mata zugi ganin yadan kumbura kaman kuma bai kumbura ba yasa tadago kanta ahankali, ganin waya kusada ita dakenan kaman nata amman banata bane yasa ahankali tasa hannu ta dauki wayan tajuya wayan tana kallo, exactly irin iPhone dinta daya siyamata ne kawai nashi white ne, danna screen din tayi kaman mai tsoro ganin baida password yasa tashiga wayan dasauri tarike bamata san inda zata shigaba, turo baki tayi aranta tace koda yaushe danne danne yake awaya nan bari muga meyake dannawa, calls dinshi taje yawancin wayanshi daga Sharif sai Ammi sai ma'aikatan shi data lura yana kara EPIC akarshen sunansu kafin idanunta su sauka akan contact din dataga yay saving da rings guda biyu, just like yanda yake awayanta dasauri tashiga contact din taga kiran datamai jiya but just to be sure number tane saitai dialing aiko saiga wayanta na kara dake kan side drawer, katse wayan tayi ahankali tace "kome zobe guda biyu ke nufi oho, nine zobe" hararan wayan tayi tafita watsapp dinshi ta shiga duka office chat ne maganan kudi shikenan, saikuma chat din wasu numbers dabaimayi saving ba, bama yabude chats din ahankali tasa hannu tabude chat din watace tamai message sunanta Fareeda tana sonshi yacemata married da 2 rings agaban married din, tsayawa tayi tacigaba da kallo yarinyar taga tacigaba damai message taji ya aureta tazama nabiyu but tun bayan reply din dayamata bai kara bude message din ba inba ita data bude yanzu ba sauran number ma haka duk yace musu married sosai abin yadan bata mamaki, amman agida ai nuna yake baimasan yay auren ba, fitowa tayo ta shiga normal text message dinshi yawanci alert na nakudi, kudin account dinshi tama kasa fadin kudin dan yafi karfin kanta fita tayi sanan tashiga gallery dinshi, wani irin freezing tayi dan tana shiga hotunan ta ne sukai popping out, hotunan ta na dayan wayan daya karba dabama tasan inda yayi da wayan ba koyabama Grandma abinta ne oho, sosai tai mamakin hotunan, tanata kallonsu one by one saikuma tadanyi murmushi kusan wannen ne the first abu dayatabayi yasa tai murmushi, kofanta dataji antaba yasa dawani irin sauri tadaga filo ta tura wayan akasa, Grandma ne tashigo tana kallon ruwan tace "ohh idanunki biyu tun yaushe kika tashi, ruwan ma yakare bari nakira Asad din yazo yacire miki zakiyi fitsari ko?" gyadamata kai tayi ashagwabe tana turo baki, Grandma datasaki baki tana kallonta tace"yau kuma da shagwaba kika tashi bari mijinki yazo kimishi danni ko kallonki bazanyiba yarinya" turo baki tayi duk idan ankirashi da mijinta wani iri takeji, dialing number shi Grandma tayi takara wayan a kunne, kara da wayanshi yafara adakin yasada sauri ta saukar da wayanta daga kunne takalli Du'a da kanta ke kasa tana wasada yatsunta tace "yanzu sabida bakin hali wayan Asad na nan dakin kikai shiru kina kallona ina kiranshi" sake turoma Grandma baki tayi takauda kanta gefe tace "aini bansan wayanshi bane, akarkashin filo nagani" wani kalan murmushi Grandma tayi ta girgixa kai tace "ai shikenan bari nakira Sharif ya turomin shi" takai wayan kunnenta saida tagama waya da Sharif sanan ta ijiye wayan bayin ta tashiga tafito dawani baho da brush da makilin tace "yi brush kafin yazo to" ahankali takarba tafara tana yatsine fuska dan bakinta ba dadi ko kadan, saida tagama sanan Grandma tawuce bayinta tana ciki aka turo kofan dakinta ahankali dayasa tadaga kanta dasauri, hada ido sukayi da Asad dake sanyeda wani white jallabiya daya haska shi sosai, dauke kanta tayi dasauri batare data kara kallonshi ba daidai Grandma tafito daga bayi ganinshi tsaye wajen kofa yasa tace " shigo Asad, gatanan kafin tamin fitsari agado kasanta da shegen fitsari kaman kaza" dagokai Du'a tayi tai wani rai rau da fuska kaman zatai kuka tana kallon Grandma din, dasauri Grandma tadaura hannunta kan baki tana kallon Du'a cikeda neman tsokana tace "kaji Asad bata fitsari kaman kaza amman dududu yaushe Du'a tama dena fitsarin kwance" cikeda kulewa Du'a dake gab da fashewa da kuka tace "Grandmaaaaaaa" dasauri Grandma tace "tona barmiki dakin tunda korona kike" tabita gefen Asad dake jinsu ya tsuke fuska kaman badariya yakeji ba, saida yaga tashiga dakinta sanan ya janyo kofan yashigo yana kallonta yanda ta turo baki tana kallon wani gefe, ahankali yasa hannunshi yakama hannunta dasauri takalleshi dan duk in yatabata saitaji wani iri, shima kallonta yake, ruwan yazare yace "go and pee" daukekai tayida sauri cikeda kunya dakuma haushi da kumburewa tace "ni banaji" wanan karan saida yay dan murmushi sanan yace "okay!" ahankali ya tsugunna agabanta yakama kafarta yana kallo na kusan sanan yadaga kanshi ya kalleta ganin har lokacin wani wuri take kallo yasa yadan cije lips dinshi sanan ya danne wajen kusan ihu tayi tawani irin mike tsaye tana karban kafan takai hannun tadaura kan maranta tanadan kuka amugun shagwabe looking damn cute, ahankali yana kallonta da idanunshi dasukai kananu yace "u want to pee now"? gyadamai kai tayi ahankali, ahankali yace "okay go" juyawa tayi zata tafi harta daga kafanta mai lafiya zata daga mara lafiyan ta tsaya tasake raurau da idanu, ahankali yace "what"? Murya chan kasa tace "my leg" bin santala santalan cinyoyinta yayi da kallo kafin cikin wani irin murya kaman batashi ba yace "in kaiki"? Makemai kafada tayi kaman wata yar baby shi tace "Grandma" dan murmushi yayi yakalleta yanda taki kallonshi all this while kawai jitayi an dauketa, dasauri ta kalleshi adan tsorace gira daya yadaga mata yafara tafiya da ita har cikin bathroom din dabai taba shigaba sanan yadauketa sanan yabi bayinda kallo so clean ga Bra dinta da pant da Grandma ta wanke mata jiya ta shanya, sauke kanta tayi kasa tana wasada yatsunta, murya chan kasa while staring at her yace "bazaki yiba" dan turo baki tayi murya ciki ciki tace "ai baka fitaba" karasowa yayi gabanta ya tsaya, hannunshi yakai yadaura akan bakinta yadan murde dayasa tasaki wani shegen kara tana kallonshi kaman zatai kuka, fuskanshi yakai dab da nata yace "if u do this for me again saina baki mamaki" yay maganan yana sakin bakin sanan yajuya turomai bakin tayi kaman yasani yajuyo dasauri tasaukar da kanta kasa, wani dan murmushi yayi yabude kofa yafita, saita tadan bata lokaci sanan tai fitsarin tayo alwala tana tsaye a inda yabarta taki tafiya bawai kuma bazata iya tafiyan bane kawai tsoron taka kafan take, murya chan kasa ciki ciki tace "nagama" ga mamakinta dan bata zaci yana kusaba turo kofan bayin yayi yashigo yana kallonta daukanta yayi kaman baby sanan yafito da ita akan gadon ya daurata ta zauna sanan yadauki dogon hijabinta daya gani kan kujera yasamata sanan yakoma wajen ledan magungunan ta yana ciro abubuwa hakan yasa tai salla awajen azaune, saida ta idar sanan yazo rikeda allura a hannunshi yace "kwanta" ahankali ta kwanta jikinta narawa kankame filo tayi ta runtse idanunta gamgam, tsayawa yayi yana kallonta kafin yay dan murmushi yadaga riganta sama, red lace pant din datasa awanan farin bombom din yabida kallo, wani muguwan ijiyan zuciya yasauke sanan yamata alluran yaja riganta da sauri yasauke kafin ahankali yace "sit up" daidai lokacin anyi knocking kofarta, murya chan ciki yace "come in" bude kofa akayi Razika tashigo da tray na shayi da chips saikuma peppered chicken, tashi tayi ahankali ta zauna dan bamatasan yay alluran ba, gaishesu Razika tayi sanan tawuce tafice kanta akasa, kusada ita yazauna sanan yadauki tea yasa spoon yadeba yakai bakinshi jinda zafi yasa yafara juya tea dan yahuce, ahankali take kallon naman da kamshin shi keta shiga mata hanci da dagokai tayi takalleshi ganin juya tea yaketayi yasa ahankali tasa hannunta tadauki cinyan kaza tagutsura ahankali wani kalan murmushi tasaki jin da dadi sanan tacigaba daci dasauri ita tana manta da mutum kusada ita, ijiye kashin tayi tadau na biyun ta shiga ci, tasake ijiye kashin tadau na ukun kafin kaceme tacinye sanan tasa hannu tadau 4th naman wanda shine na karshe tafaraci hakanan jikinta yamata kaman ana kallonta juyoda kanta tayi ahankali takalleshi hada ido sukayi ya tsaya chak yana kallonta this time fuskanshi yanuna mamaki, ahankali takai naman ta ijiye akan plate din murya chan kasa tace "sorry" dan murmushi kawai yayi yamika mata tea a mug yace "drink kisha magana" sanan yadau tray yasa mata akan cinya yace "and eat d chip" gyadamai kai tayi ahankali kai tea baki tayi ta kurbi kadan ta hadiye tana yatmutse fuska sanan tadebo chips din guda biyu kadai takai baki ahankali take tunawa kama ganin yanda takeci kasan bataso sanan ahankali tadago kanta ta kallai ganin kallonta yake yasa murya chan kasa kaman mai tsoron fadimai tace "nakoshi Ya Asad" wani kalan mugun kallo dayamata yasa tamaida kanta kasa tadau tea tacigaba da sha tanacin chips din ahankali ganin tadanci yasa yasa hannunshi ya karbi cup din da tray fin ya ijiye kan side drawer sanan yadauki plate da namanta kekai yabata yace "eat your meat" dago kanta tayi takalleshi ganin fuskanshi looks simple yasa ahankali tasa hannunta tadauki naman sanan taiwani irin murmushi da saida abin yama bashi mamaki tashigaci tana murmushi tass tacinye dan juyarda kanshi yayi yay murmushi sanan yajuyo yakalleta kaman baiyiba,tissue yabata ta goge hannunta sanan yakawo maganin ta yabata karba tayi tasha still tana murmushi. "where is my phone" dago kanta tayi takalleshi kaman wacce bata gane meyake cewa ba, saikuma ahankali tasa hannunta akarkashin filo tadauko wayan tabashi karba yayi yakalli wayan batare daya budeba yadago kanshi yakalleta fuskanshi babu alamun wasa yace "why did u go through my phone"? Kallonshi tayi gabanta nafaduwa rawa lips dinta yafara rasa abinda zatace yasa ahankali tace "sorry I thought nawa ne" hararanta yayi sanan yasa wayan a aljihu yawuce yafita daga dakin, yasauka kasa a falo yaga Rahima da Grandma suna hira abinsu, ganinshi yasa Grandma tace "Ya jikin nata takoci abincin? Ni banmaso Razika tasa mata nama ba wlh dannasan naman zatabi ta tsince duka yarinyar nan bazata ci abinci ba" yatsine fuska yayi kaman baiso yay magana atakaice yace "yau zataci abinci" sanan yawuce yafita Rahima tabishi da kallo wani abu namata yawo arai, tashi tayi tawuce tai sama tace "ni wajen kanwata nazo ba wajenki ba Hajiya natafi" tabe baki Hajiya tayi tace "au haka kikace zoki barmin gidana to saiki bari idan aka kaita gidan wanki Asad saiki dinga zuwa chan" Dariya t 3rd ayi tawuce abinta batare datace komiba. 5️⃣6️⃣ Da Sallama tashiga dakin zaune taga Du'a akan gadon, daga ita sai wata yar jan riga data tsayamata acinya, anmata parking kalabanta tai wani irin simple kyau tana daddanna wayanta da babu wani abun kirkin datakeyi dashi, ganin Rahima yasa tai wani kalan murmushi tace "Ya Rahima kinzo good morning" karasowa tayi tazauna abakin gadon tana kallon kafan nata that looks good tace "sannu ya jikinki? Ya kafan yadena zugin" gyadamata kai tayi ahankali batare datai magana ba, kallonta Rahima tayi Du'a is really a definition of innocence, zama tayi kusada ita ta jingina da bangon gado tace "kinsan gobe Ammi zata tafi Dubai za'a je ahado akwatin ki, yaushe zaki fitomana da anko yanzu fa yau bikin ku saura sati uku da kwana shidda" kallonta Du'a tayi gabanta nafaduwa kaman bazata ce komiba saikuma ahankali tace "wai dagaske Ammi take? Ni banson Ya As....." kaman wacce ta tuna abu saitai shiru tana kallon Rahima dake kallonta gabanta nafaduwa, murmushi Rahima tayi saikuma ta tashi takama hannunta tarike tace "Du'a kinsan ni na yarinya bace ko I am 27 yanzu, inaso nagama school ne this year da tuni mai aure nima, inaso ki gayamin gaskiya because I really want to help u tsakani ga Allah, I told you zan zame miki sister dabaki taba samuba in your life, and duk wata magana da zamuyi it will be tsakanin mu me and u har abada, I want to help u so tell me now how did everything happen har kika auri Ya Asad bayan baki sonshi? I promise bazan fadamai ba or anybody" tunda Rahima ke maganan take kallonta hakanan taji ta yarda da ita itama kuma tanason tagayama wani labarin koya rage nauyi daya mata azuciya, murya chan kasa tace "Ya Rahima ni wlh banason Ya Asad, wlh ko mugun tsoron shi nakeji, ko yanzu ma sabida nasan agidane akwai Grandma da kowa bazai iya min mugunta ba ko yaci zaluna, amman idan akai bikin ba barin gida akeyi ba za'a kaini gidanshi ko"? ta tambayi Rahima, gyadamata kai Rahima tayi hakan yasa tace "wlh ni banaso, Ya Asad baida kirki mugu ne, shi yace ince ina sonshi ni bana sonshi ko kadan......" gabaki daya tabama Rahima labarin yanda akai auren, bakaramin mamaki tayiba, from what she understands a labarin nan Ya Asad na mugun son Du'a amman shegen halinshi na zurfin ciki, da jan aji da mugunta boyewa yake yana nunama mutane kaman ana tursasashi ne aiko yanzu zai gane, gani yanda Rahima ke murmushi yasa Du'a tace "why are you smiling" girgixa mata kai Rahima tayi tace "babu komi, kawai mamakin rashin wayonki nake, all I will tell you is Ya Asad na bala'in sonki and kibari ayi bikinku karkice komi kinji Du'a" gyadamata kai tayi idanunta sun kawo kwalla, dan hararanta Rahima tayi tace "I will teach u yanda zaki handling Ya Asad cikin ruwan sanyi kawo kunnenki kiji" dasauri Du'a takai kunnenta, magana Rahima tashiga mata whispering, dasauri tadago kanta takalleta idanunta awaje gabanta nafaduwa tace "Ya Rahima no bazan iyaba wlh, tsoro nakeji" hararanta Rahima tayi tace "bakiso ki chanza ko kinfison mutane koda yaushe nacin zalinki ana taking advantage of you, wlh bazai miki komiba yana sonki zaki gani kinji" gyadamata kai tayi jikinta yay sanyi, Rahima tai murmushi tacigaba da gayamata maganganu akunne daga wanda Du'a zatai rejecting sai wanda zatayi kaman zata fashe da kuka saida Grandma tazo takadata kan taje tai wanka sutafi kan Ammi takira ana neman ta sanan ta tafi ranta fess takasa daina mamaki bata taba ganin takadirin mutum irin Ya Asad ba, saisa kowa ke cemai mai bakin hali, cikin ruwan sanyi yama Du'a wayau ya aure ita banzan Du'a bama tasani ba batasan yamata wayau ya aureta bane sai uban tsoron shi datakeji kaman wani ma'aikata, kiri kiri yasa yarinya tai rashin kunya tace ita aure takeso shi takeso shiko yana gida yana cincin magani Ammi kullum cikin lallabashi take yanayi kaman forcing nashi akayi ya aureta duk basusan yaron su yay lakur shiya hada komi ba Kai Ya Asad nacire maka hula awanan act din, Rahima tafadi tana murmushi, Ya Asad Ya Asad shegen guy ne wlh, amman yanzu duhun shi yacika, bazai karama yarinya wayau ba wlh, dan wlh saita zuga Du'a tasa yamugun susuce ya rame I will make Du'a beat u in your own game, niko nace to masu karatu kuna ganin Mr Asad Abdullahi Kitse is beatable kuwa???? Let the show begins. Bai kara dawowa gidan ba saida daddare wuraren karfe tara na dare, koda yashigo gidan babu kowa a falo hakan yasa yay sama, ahankali yay knocking dakinta tareda budewa yashiga ciki tana zaune kan gado waya akunnenta tana murmushi, kallo daya tamai tadauke kai tana murmushi wanda da alamu awaya ne take murmushin, ahankali cikin yar muryanta tace "ai yama dena zafi yanzu ciwon dakace haka" hakanan yaji kirjinshi yabada dumm! Dakace haka! yamaimaita aranshi saikuma yakalleta, hannunta daya yaga tadaura akan fuskanta tana murmushi tace "ni ba baby bane kadena cemin baby I am 22 fa" tawani turo baki sosai, hakanan yaji kafarshi yasoma rawa yana shaking zuciyanshi nawani irin tafarfasa yama kasa tafiya tsabagen yanda zuciyanshi ke tafarfasa yana kallonta, dariya yaga tahauyi sosai taja fito ta kankame ashagwabe tace "ohh'ohh ni sainakai 25yrs ko 27yrs zanyi aure" kulewa yaji idanunshi sunyi rufff yawani tako zuwa gabanta kawai mutum taji ya kanta yawani irin fizge wayan dake kunnenta yawani chill wayan bango wayan ya tarwatse da hannunshi biyu yasa yawani jawo gaban riganta ya mikarda ita tsaye shaketa yayi da rigan idanunshi sunyi jajir yace "da ubanwa kike waya kina matasayin my wife ha" rawa sosai jikinta yafara kafanta yashiga rawa tana zaro idanu tana kallonshi yanda taga yayi yasa taji zuciyanta kaman zai fashe sabida tsoro tama kasa magana, cikin wani irin murya kaman wanda aljanu yashiga yace "so u are calling a man kina gayamai kinji ciwo lallashinki ma yake kinamai shagwaba eh, kinsan akwai aurena akanki u want me to kill you" bubbuga hannunshi take alamun yasaketa amman ina yakasa sakinta, tuna abinda Rahima ta gayamata tayi da kyar tadaure ganin tana nema tamutu tace "to ai ba aure mukayiba nika sakenmin wuya, I am nobody's wife" wani irin rawa hannunshi suka shigayi yana kallonta kungane irin maganan nan dazakajita daga bakin wanda baka taba expecting ba hakan yasa kaji duk wani energy na jikinka yay draining yakare that's the same situation da Asad yashiga baisan lokacin daya saketa ba hannunshi narawa sosai, tari tashigayi tana kuka idanunta sunyi jajir ta duka tana Tari, Asad yadade yana kallonta jikinshi still rawa yake sanan cikin wata irin kakkausar murya yace "what did u just say"? daurewa tayi ta tashi ahankali tana shafa wuyanta takalleshi tsayarda kukan datakeyi tayi tace "nace niba matanka bane, I am not your wife, wanan auren dazuwa masallacin dakukayi aka daura everything is fake ai taimakona kayi sabida karsu Abba su tafi dani, kuma sukazo basu tafi dani ba ba shikenan ba, ni bazan taba aurenka ba, bazan zauna dakai ba, ni bana sonka kaima baka sona Dad yace rokonka Ammi tayi ka yarda, ni wlh baran aureka ba" Asad is someone dazata iya cewa bata taba iya tantance yanayin fuskanshi ba but yau zata iya fassara abinda tagani a idanunshi da fear, sosai jikinshi yahau bari yana kallonta yanda take kuka tsaye agabanshi tana bubbuga lafiyayyen kafanta akasa cikeda rigima, gyadakai yayi ahankali yay wajen wayanta daya jefa da bango dagata yayi ganin ta runtse abaya da gaba amman screen din na haske still yasa ya tattaka wayan kaman ba kudi yasa yasayeta ba saida yaga screen din yadena haske sanan yadago yajuyo yakalleta har lokacin kuka take tana kallonshi kaman ba Du'a dake tsoronshi ba yawuce yabude kofa yafice, cigaba da kukan tayi tana shafa wuyanta sanan ahankali tahau kan gado tana share fuskanta tana mamaki daman zata iya dama zata iya? Abin ya bala'in bata mamaki, saikuma ahankali takalli wayan tana cikin waya daya Hamad, dazun nan fa Grandma ta shigo takarbi number shi daga hannun Grandma ta kirashi kuma ganin Asad yasa duk tai abubuwan nan, wani kalan murmushi tasaki sanan ahankali ta lumshe ido tana jiran gobe tayi tabama Rahima labari. Abangaren Asad wasa wasa har 3 bacci yakasa kwasheshi, sosai gabanshi yake yankewa yafadi, to a ina tasami saurayin datake waya dashi? Waye shi? baison yay tunanin Sharif ne dan yasan bashi bane tundaga ranan da aka daura aurensu yama daina kula Du'a to waye?? Yanda abin ke damunshi ma yasa yaji kanshi yasoma sarawa sosai baimaso yay imagining abinda yahana ayi bikin nan akaita gidanshi how he has waited for that day, yanzu da opportunity yazo Ammi dakanshi tazo ana lallabashi kan ya yarda this girl wants to fuck it all up for him, wasa wasa har asuba Asad bai rubtsa ba kanshi nawani irin mugun ciwo kunsan futunannun yara da suka saba fitinan mutane randa su aka fitinesu basu iya handling abunba sosai zazzabi na neman rufe Asad dan yama kasa tashi yaje sallan asuba, bayan Sharif yashigo gidan daga masallaci ne da shima yamakara saisa baima lurada Asad baitafi ba, dakinshi straight yawuce ganin baiganshi a mosque ba, ahankali yabude kofan ganin Asad zaune kan gado da singlet yakama kanshi yarikeda hannu yasa dawani irin sauri yay cikin dakin hannunshi yakai yataba wuyanshi jin zafi yasa dasauri yakalleshi yace "Asad bakada lpy subhanallahi meke damunka" da hannunshi yanunamai kanshi hakan yasa Sharif yace "sannu, tashi ka lallaba kai salla saika fadamin maganin dazan siyomaka" yay maganan yana dagashi, da kyar ya iya mikewa tsaye yadan bude idanunshi kadan saikawai duhu daganan baisake sanin inda kanshi yakeba. Ahankali yake bude idanunshi kadan kadan, kafin yagama budesu duka, Dad dinshi yagani kusadashi yarike hannunshi cikeda damuwa, sai Ammin shi zaune a gefen Dad din tabuga tagumi tana kallonshi idanunta sunyi ja sosai, sai Sharif dake tsaye tareda likita yanamai magana, sai Anty Turai dasu Rahima gabaki dayansu babu wanda ya lura dayama farka, motsin dayayi yasa Dad yatashi dasauri kanshi yana shafa soft coil gashin shi yace "Son are u awake? Can u hear me" dasauri Dr dake tareda Asad yazo kanshi yataba kanshi sanan yace "Asad can u hear me" bude idanunshi duka yayi ya kallesu sanan yay yunkurin tashi zaune yace "I am fine maisa kamin fixing drip" dasauri Dad yatareshi shima tsayawa yayi jin kanshi yasara, Dad yace "please son don't be stubborn kanka na bala'in ciwo, Dr yace u need to rest stress yamaka yawa" yatsine fuska yayi yajuyar da kanshi shifa baiso ataru ana kallonshi sabida yanadan ciwon kai, ranshi abace yace "Dad to kutafi please niku barni da Dr kun cikamin daki, those children should get out" murmushi Rahima tayi tai kwafa taja su Mariya duk suka fice,Anty Turai ta ballamai harara tace "ai dabaka so aga kana rashin lafiya dabaka sumema mutane ba sabida dan ciwon kai, lazy man sai uban wearing strong man's face ciwon kai yasa yasume mtswww" tawuce tafita, juyodakai Asad yay yakalli Dad dayaga yay murmushi yace "yakuri yazakayi she's ur aunt" dauke kai yayi cikeda fushi, Dad yatashi yakalli Ammi yace "zokiga muje tunda danki kunya yake muganshi baida lpy" ahankali ta tashi tana kallon Asad din daya juyamusu baya suka wuce suka tafi sanan Sharif yakalli Dr yace "bari nabaka wuri kayi magana da patient dinka, please Jabir kama abokinka fada kadaiga irin halinshi" yawuce yafita tareda rufo musu kofa yasauka yafice danyaje yadebo mai abinci tunda yafarka. Abakin gadon Jabir yazauna wanda tare sukai school da Asad din abokin shi ne a school, dayake Asad bai iya keeping friends ba saisa they're not that close, ahankali yace "u can turn around now I am d only one adakin let's talk" ahankali yajuyo yakalleshi yace "hope baka fadamusu abinda ke damuna ba" ahankali Jabir yace "so kasan abinda ke damunka Asad" yatsine fuska yayi, cikeda mamaki Jabir yace "Asad wai har yanzu kana nan da halin nan? Anyway that aside kaje kar aure kar family ka dake mugun sonka dinan wata rana su wayi gari suga gawanka adaki, banda haka anything dazai saka damuwa koke baka damuwa ka gujeshi, damuwa na tadaka, tadaka kuma na sakin maka bala'in magrine" yatsine fuska yayi yace "nariga nai aure already so it's not a big deal I can handle din, kawai kacemusu ciwon kaine" gyadamai kai yayi sanan yaciro wasu magunguna daga aljihunshi yamikamai yace "da Sharif yakirani nazo nadubaka saida nakara fita I got this drugs for u banbashi ba dan zai iya ganewa, so kadinga sha, and avoid any matsala da damuwa da abinda zai tayarmaka da hankali please" gyadamai kai yayi ahankali yakarbi maganin yace "thanks" sallama Dr yamai sanan yawuce yatafi lallabawa yayi yatashi yana tafiya ahankali yashiga bayi alwala ya dauro yazo yay salla sanan ya kwanta Sharif yakawomai abinci yaci kadan. Wasa Wasa yau 2weeks da kwana 6 kenan Du'a bata kara sashi a ido ba, dudda Grandma tacemata baida lafiya, Rahima ma da kullum saitazo tagayamata baida lafiya ne amman ya warke yakoma office, gashi yakara komarda ita square one batada waya kuma, tuni kafarta ya warke ancigaba da mata gyara na ban mamaki, Grandma sai shirin biki take gadan gadan itace uwa itakuma ce uba wajen Du'a ko sau daya bata taba kiran Abba tace mai yakawo kudi tasiyamata kaza ba, tasai kirasu amatsayinsu na iyayenta tagayamusu anyi fixing ranan biki tafadi musu ranan, amman ita ke komi, Alhamdulillah tanada kudinta sanan danta Muhammad yayan Mami yakara aikomata da millions tai hidiman biki sanan shida matarshi da yaranshi duk zasuzo habawa zokaga shiri har fentin gidanta ake sakeyi zata aurar da jika, Du'a harwani sheki take ga kamshi kaman ba gobe, magungunan ko karamata kiba suke oho amman har wani cika take tana karawa fatarta yakara laushi da haske, sai idanunta ne dasukai zuru zuru itafa bama wai zigin Rahima ba koda bata Allah yasan batasan auren nan to ai auren wayaune ba aureba gashi bata karasa Ya Asad din a ido ba kuma batada waya. Sosai Grandma kesaa_ girki kuma Alhamdulillah ba laifi tadan iya sosai. 5️⃣7️⃣ Duk wanda zai shigo estate dinan saiyasan akwai babban biki za'ayi sabida yanda har estate din an gyara yau duka duka bikin saura 6days, yau tunsafe Rahima da Mariya sukazo suka dauketa banda Aneesah rabonta dataga Aneesah harta manta abinma nabata mamaki, Grandma basu hanasu fitada itaba dan al'adace idan za'a kawo akwati Amarya tagudu daga gida, mota suka shiga Rahima ce taja suka fita shagon hudayya fitting, suna shagon wajajen one wayar Rahima tai ringing daukan wayan tayi daga yanda take amsa wayan anatse duk suke kallonta, saikuma ahankali tamikama Du'a wayan kallonta tayi tana ware ido tace "waye" da baki tamata alamu Ya Asad ne, ahankali takarbi wayan tasa akunne murya chan kasa tace "Hello" cikin kakkausar murya yace "did I give u permission to go out" dan faduwa gabanta yayi tarasa wani kalan shakkan Ya Asad take dako magana yamata sai gabanta yafadi sabida muryan shi, kasa amsashi tayi cikeda bata rai yace "come out ina parking space" ahankali tazare wayan daga kunne tamikama Rahima looking sad, katse wayan Rahima tayi takalleta tace "meyace" ahankali tace "yace ina kasa wajen parking na same shi awurin" tai maganan ko kadan fuskanta babu alamun farin ciki, murmushi Rahima tayi tace "tashi kije karkiji tsoro ki karamai maganan ranan nan harda wanda na gayamiki jiya" Kallon Rahima Mariya tayi tana mamaki wani magana, tashi ahankali Du'a tayi tadau karamin gyalenta ta yafa kan doguwan rigan atampan data saka blue dayamata chass ajiki, ko Grandma ma hayaniyan daya cika kanta ne dasaita hanata fita dashi tasata tasaka abaya dan bata barinta fitada kaya haka sabida yanda suke nuna suranta, tundaga sama tahangoshi a parking space tsaye yasaka wani farin yadi jumper yay wani irin kyau bakinshi na kyalli lips dinshi sunyi pink sosai, gashin kanshi sunyi coils sosai suna kyalli arana, idanunshi yasanya bakin glasses yay folding hannu akirji kaman wani soja, turo baki tayi tana tafiya ahankali rabonda tasashi a idonta harta manta dan tun ranan nan, hakane baida lafiya bai rameba saima wani kyau daya kara, bude kofa tayi tafito tana tafiya ahankali, tunda tafito yake kallonta ta cikin bakin glasses din idanunshi ranshi yay masifan baci, gabaki dayan suranta ana gani gashi dogon rigan yamata bala'in kyau, dan gyalen data yafa kusan rabin gaban gashinta abude dayake atsefe anmata parking dinsu yana ganin jelan gashin daga ta bayanta kaganta zaka dauka wata yar shugaban kasane, security wajen sai satan kallonta suke ita bama tasan sunayi ba sai dumfaroshi take tana tafiya ahankali, ganin tana tafiyan kaman bazatayi ba mazan na kallon bayanta yasa yawani taho da sauri tsayawa tayi jikinta narawa, hannunshi yasa yawani fizgota yashiga bayanta sanan yakalli security yace "you are about to loose tunda matan mutane kake kallo stupid goat" dasauri security yadauke kanshi gefe yawuce da sauri yashiga ciki jikinshi narawa. Batare da Asad yakalleta ba yawani jaa hannunta gaban motan yabude yaturata ta zauna sanan ya tsaya akanta dukan motan yayi da hannu cikin fushi yace "are you mad dazaki fito haka half naked eh?" Yasake buga hannunshi amotan dayasa ta runtse ido atsorace tarasa metama mutumin nan shidai yamata fada yaji dadi, maida kofan yayi yarufe da karfi dayay kara takara firgita sanan yazagaya yadawo mazaunin direba ya zauna yatada motan yajaa, har yakai anguwansu baice mata komaiba itama batacemai ba, sanin ana gidansu anjekai akwatin yasa yawuce gidansu da ita har gaban flat dinsu yakai motan sanan yakashe yafito yarufe yazagaya ta side dinta yabude motan yana kallonta yace "come out" ahankali tafito daga motan yawuce kofa yabude yashiga hakan yasa itama tabishi ta shiga, uban kati tagani akan kujera dawani hadadden karamin box, da bandir na kudi daban daban dabama tasan yawansu ba yanuna mata da hannu bayan ta shigo tamaida kofan tarufe yace "this are all ur things ki kwashe kibar nan wajen" yay maganan yay stairs, kallon abun tayi tasan abubuwan biki ne sanan tadagakai ta kalleshi, rawa jikinta yafara but tadaure ahankali tace "ni babu abinda zanyi dasu, ni baruwana banmasan shirye shiryen bikin wa akeyi ba, aina gayamaka ranan katafi bankara ganin ka ba saiyau, ni bazan aureka ba dan banasonka" tunda take maganan ya tsaya chak, sanan ahankali yajuyo yakalleta, hannunshi yasa kan glasses din idanunshi yacire yakalleta, dauke kai tayida sauri tana wasada yatsunta, saukowa yashiga yi daidai karshen stairs din ya tsaya yana kallonta gabanta nafaduwa yana kallonta still yace "what did you just tell me"? kasa magana tayi kirjinta na mugun bugawa dan yanda takejin muryanshi kaman zai doketa, ganin yanda jikinta kerawa yasa ya girgixakai kawai yajuya yafara tafiya, ganin yajuya yasa murya chan kasa atsorace tace "wlh yanzun nan zanje nagayama Ammi da Dad dakowa abinda yafaru ranan, sabida a fasa bikin nan ni baran zauna dakaiba" tai maganan tana juyawa tai wajen kofa, chak ya tsaya gabanshi na dukan uku uku yasan Du'a bawani hankalin kirki ne da itaba yarinyar dayasa ta iya gayama ubanta aure takeso zata iya zuwa tafadi komi yanda yafaru, dawani irin sauri yajuya yasauko bude kofa yayi yafito Allah yasoshi babu kowa a compound dan duk ana gidan Hajiya Ammi ne kawai yasan ba'a je da itaba, hartasa hannu zata bude kofan falonsu taji an fizgota zatai ihu yasa hannunshi akan bakinta yadanne yadauketa chak, tana ihu amman babu maiji flat dinshi yashiga ya ita yamaida kofan yarufe yasa key sanan yay sama da ita tana shushure kafa tana kokarin kwace kanta, da kafanshi yabugi kofar dakinshi azuciye yashiga da ita sanan yawani irin jefata kan gado yana datse kofan dasauri ta tashi dagakan gadon jikinta ko'ina nabari, hannunshi yakai kan boturan riganshi yana cire wa yana mata wani irin mugun kallo yace "ni kikema tsiwa kina gayamin zakije kifada Ammi da kowa komi" wani irin rawa lips dinta yafara sosai jikinta ko'ina na bari ganin yanda idanunshi suka juya kaman yay shaye shaye, rigan yacire ya yar, wani irin ihu tayi tadaura hannayenta biyu kan fuskanta jikinta narawa sosai takasa magana, wandonshi yacire shima ya yar yacire singlet ya yar yarage dagashi sai boxer sanan yasa hannu yakashe wutan dakin dakin yay duhu kaman ba rana ba, cikin kakkausar murya yace "I will never stop you from telling them everthing, but kafin kiyi bari na tabbatar najuye manni yi na amahaifanki, narabaki da budurcin ki, na tabbatar nazuba miki kwayayena acikinki nagama saikije kisa araba auren sanan kiyi zaman 9 month ki haifamin baby na, kafin kije ki auri wanda kikeso how do u see the plan" wanan karan fashewa tayi da kuka sosai ganin duhu adakin ga maganganun dayake gayamata ba shiri tace "Ya Asad yakuri wasa nakeyi, Allah bazan fadaba" wani irin jawota akayi tasauko daga kan gadon tafado jikinshi ita kanta saida taji tsoron hucin dayakeyi, wani irin fashewa da kuka tayi ta rirrikemai kafada atsorace tace "Ya Asad please I am sorry wlh ina sonka pleasessss" yatsanshi yadaura akan lips dinta cikin wani irin murya kaman na boss that is low and calm at the same time yace "shiiiiiiiiii" hadiye kukan tayi gum kaman ba itaba dan taga abinda yafi karfinta, yana rikeda ita yace "kinsan menene sex"? girgizamai kai tayi ahankali batare datai magana ba, janye yatsarshi yayi dagakan bakinta yace "bakisan miye sex ba" ahankali bakinta na shaking tace "na karanta a English novel dina" murya chan kasa yace "good! abinda zanyi dake kenan, and I promise to make it very very painful for you haka akema yara marasa kunya" kara rirrike mai kafada tayi tana wani irin kuka tace "Ya Asad wlh wlh wlh bazan karama tsiwa ba, nayi kome kaga dama kamin, dan Allah karkamin sex, please Ya Asad banso babu kyau, Ya Asad wlh wlh wlh na tub......." shiiiiiiii! hadiye maganan tayi gum jin yace mata shuuu, murya chan kasa yace "give me ur hand" babu musu tana kuka ahankali mara sauti tazare hannunta daya dagakan kafadarta tabashi karba yayi taji yakai hannunta kasa dayake babu haske taji yadaura hannunta akan wani abu kaman mucciyan da Grandma kebata ta tuka tuwo bambamcin shine wanan yafi mucciyansu kauri, ahankali yace "hold this for me" dasauri tarike da kyau jikinta narawa dan batasan me abinba tadaiji abin na nishi da motsi a hannunta, wani irin ijiyan zuciya taji Asad yasauke ahankali yace "aaahhhhhh" sanan yawani pulling jelan gashinta tabaya dayasa kanta yay baya kaman zai karya mata wuya dan wuyanta ya bankare sanan ahankali yadauko da kanshi yashiga kissing wuyanta yana wani irin nishi wani irin rawa jikinta keyi amman takasa komi jikinta namata wani yam yam, tundaga wuyanta yake kissing har wajen gemunta kafan yataho saman gemun sanan gently yashiga yay grabbing lips dinta ya shiga kissing bakinta yana kara pulling gashinta so rough dayasa tasaki kuka tasaki dick dinshi, bakinshi nakan nata yace "hold it" dawani irin sauri tarike back, kissing dinta yashigayi sosai yana shafa bayanta da hannu daya kafin yasauke hannunshi kan zip dinta yawani ja zip din kasa jikake zippppp! awani irin firgice tasakeshi ta fizge bakinta takoma baya tana kuka sosai tace "Ya Asad karka ciremin riga dan Allah" hannunshi yasa ya fizgota tadawo jikinshi back tana tureshi yace "I want to sex u and get u pregnant kafin kije kifadi abinda yafaru" cikin kuka sosai tace "Ya Asad ai nafasa wlh, wlh bazan fadabi dan Allah kayakuri I don't want sex wlh" kokarin grabbing bakinta yake tana kaucewa tana kuka murya chan kasa yace "baki fasaba please kije kifadi" matseta yayi yakama bakinta yacigaba da kissing sanan yaja rigan nata kasa yarage daga ita sai bra da pant, wani irin tureshi tashigayi da kafa tanason ta kwace kanta ganin haka yasa yaharde kafafunta cikin nashi, ya matse hannayenta both a hammatan shi duka biyun, sanan yakai hannun bayanta yana kokarin bude unhooking mata bra tashiga mutsu mutsu zata kwace kanta amman takasa da kyar ta iya fizge bakinta daga nashi tana kuka sosai tana kokarin fizge hannayenta daga hammatanshi tace "wlh bazaka ciremin bra kaganni ba" sosai kokawan datake dashi yakemai dadi, kara matse hannayen da kafafunta yayi yace "nikuma wlh saina ciremiki breziyan nan nakuma sha wanan nonon babu yanda zakiyi" wani irin rushewa da kuka tayi zaka dauka kasheta ake tana kokawan ciro hannayenta kawai yacire hook din bra din, da gangan yadan sassauta rikon dayama hannayenta da kafafuwanta hakan yasa tafizge kanta tai baya ko kadan batasan hannunshi najikin bra tagaban tana fizge kanta tai baya haka bra yabiyoshi gaba ya salubo daga hannayenta, wani irin ihu tayi ta tsugunna da sauri tana boye boobs dinta da hannu, babu abinda take kunya aduniyan nan irin aga boobs dinta, jitayi duniyan ta tsayamata chak tawani irin fasheda kuka tace "Ya Asad dan girman Allah kayakuri, wlh Ya Asad na yarda da auren bazan kara fadi maka komiba dan Allah kayakuri kayafemin Ya Asad plsssss" shi kanshi yasan ta tsorata iya tsorata but ina bazai bartaba saiya gwada mata he owns her wlh, karasa cire gajeren wandonshi dayaja kasa yayi ya yar sanan yataho inda take tsugunna tana rokonshi yace "stand up kihau kan gado nasha nono" kankame jikinta tayi tana kuka sosai, saikuma tahau ihu da duka muryanta. "Ammi, Ammiiii, Ammiiii" murmushi yayi yace "gama ihun kiran kowa na gidan nan kizo kiban nono nasha I am a patient guy, saisa nabarki kinata min tsiwa kina fita ahaka kina matan aure maza na kallonki, on top of that bama kitambayi permission dinaba kika fita, laifinki nada yawa" fashewa dakuka tayi tace "Ya Asad wlh bazan karaba har abada" ahankali yace "kin gama kiran Ammin? Ina take ta zo ta ceceki mugani" yay maganan yana daura hannunshi kan bare soft bayanta dababu komi akai, wani yirrrr dataji yasa tadaga hannayenta ta ture hannunshi kaman jira yake, dayan hannunshi taji akan boobs dinta yawani damke ahankali yace "holy shitttt" wani irin mika tayi zata tureshi dasauri yajata yasata akan gado zai kai yataba boobs din tai folding hannayenta akansu tana kuka, hannunshi biyu yasa yakama hannun nata zai bude tashiga kokawa dashi tana kuka sosai tana ihu. "kabarni karka tabani" murya chan kasa yace "idan kinga ba sha nonon nan naki nakoshi ba yau to mutuwa nayi" bude hannun nata yay gabaki daya yawani irin bankareta yakai hannun ta saman kanta ya danne da hannu daya, dudda akwai duhu bai hanashi ganin yanda boobs din nata ke bouncing ba sabida yanda take shaking trying to kwace kanta, wani irin ijiyan zuciya ya sauke murya chan kasa yace "perfect hello guys come to Dady" ahankali yakai kanshi yadaura a left one din wani irin taushi yaji baisan lokacin daya bude bakinshi yasa dan karamin nipple dinta ba yana wani irin nishi kaman rago yanashan nonon like a hungry dog mercilessly, ita tadauka tama mutu ne, tunda tai wayau something like this baitaba faruwa da itaba jin namiji kan jikinta tsirara yana shamata nononta da she always hide ariga. wani irin kuka take amman nishin da gurnanin da Asad yake yamafi kukanta kara, baitaba sanin haka shan nono keda dadi ba idan yaga yaro nashan nono abin na burgeshi he always wish shine yauko yaro yadawo harwani zukowa yake yana taunawa yana gurnani yamanta ma a ina yake, dadin dayamishi yawa yasa yama saki hannayen nata yakai dayan hannunshi yana wasada dayan nonon, kaman jira take yasaketa hannayenta tadaura akan coily gashinshi tana ture kanshi wani irin kara yayi kaman dan jariri yana kokarin fizge kanshi amman ina saida ta turemai kai gabaki daya tai wani supa ta diro daga kan gadon zatai bathroom dinshi da hannu yaja lace pant din dake jikinshi jikake kittttt ya barka pant din, bata damuba tai wani tsalle tana kuka sosai tashiga bathroom din zata rufe kofan yawani bugo kofan da kafa baya tayi zata fadi dasauri yatareta kallo daya tamai ta damke idanunta tana kuka sosai shi kanshi yasan tsoratu matuka from what he just observed Du'a don't know a man in anyway ko jikinta ba'a taba tabawa ba, da karfi yasata ajikinshi ya rungume tsam yafitoda ita ahankali in a calm lallashi tone yace "stop crying kar idanunki su kumbura babu abinda zan miki just stop crying" hadiye kukan tayi tanajin yanda ya matseta ajikinshi wani abu na nushinta a mara kaman karfe tanajin yanda zuciyanshi ke bugawa, murya chan kasa yace "I will not touch ur boobs again calm down your heart is over racing" kokarin fita daga jikinshi take sabida batason yanda jikinshi ke taba nata ganin haka yasa yasaketa yazaunarda ita abakin gado yace "lemme even put on my cloth calm down" boxer shi ya laluba yasaka da kyar sanan yadau singlet dinshi yajefa mata ajiki yace "put this own" dawani irin gudu tasaka singlet din tana goge fuskanta, ganin haka yasa yadawo kusada ita yazauna yace "inada punishment ma yara marasa kunya, and I know how to fight dirty kidinga jin magana ta kina kiyaye bacin raina kinji" gyadamai kai tayi ahankali, da muryanta dahar yafara shake wa tace "sorry bazan karaba" shiru yayi shi kadai yasa abinda yakeji, murya chan kasa yace "ki kwanta to" kwanciya tayi gabanta nawani irin faduwa gwanin ban tausayi, kafafunta na kasa kin hawa dasu tayi. Murmushi yayi yasauka dagama kan gadon hakan yasa tasauke ijiyan zuciya, ta wajen kafanta yazo yakama gwuiwanta biyu yace "bude kafanki nadauko shoes dina daga karkashin gado" babu abinda yazo ranta budemai tayi ahankali, dayake fuskanta nachan tsakiyan gado ko kadan bata lura dashiba, jin kaman abu mai sanyi sanyi nabin clit dinta yasa takai hannunta sai cikin gashin kan Asad kaman jira yake yadanna fuskanshi gabaki daya agabanta dake fi_ar dawani kalan charming charismatic scent, wani irin zabura tayi tamike zaune tana kwala ihu. 5️⃣8️⃣ Wani irin nishi take numfashinta na neman daukewa dan what she is feeling right now is something da bama tasan akwaishi aduniyan nan ba, tun muryanta nafitowa harya dena wani kalan suma tayi da gatanan gatanan kawai takejin kanta tafada gadon, Asad tried his best yabarta amman yakasa sabida kamshin dakowani bangare na jikinta keyi is mind blowing, da kyar ya iya yaciro kanshi yatashi maranshi nawani irin kullewa ahankali yahau kan jikinta yana manna fuskarshi anata, murya chan kasan makoshi yana kiran sunanta. "Du'a, Du'a, Baby" jan janta yayi kafafuwanta suka hawo kan gadon yana kara ware mata kafafun sanan yasata ajikinshi ya matse kam kam yakai hannunshi yawani ja ribbon dinta ya yar yacusa hannayenshi biyun agashin yana hargitsawa sanan ahankali yakai dick dinshi to the hole yana mata nishi a kunne yana kara Kankameta yana wani irin nishi kaman zai fashe da kuka, ko alamu akwai rami awajen ma baiji ba dan amugun rufe kofan yake dannawa yayi da karfi dayasa tabude ido tareda bude baki zatai ihu dasauri yacire fuskanshi dagakan kunnenta yashiga kissing nata yana sake second attempt, wani irin uncontrollable kuka take abakinshi ganin haka yasa shima yana rude he's just trying to cum koya sami sauki amman yakasa yana rikeda ita yatashi yaja drawer shi yadauko magani sanan yasaki bakinta tasake fashewa da kuka maganin ta jefe abaki ya hadiye sanan ya ijiye ya kankameta tsam tsam yana shafa bayanta yace "shiiiiii stop crying" shiru tayi tana wani irin sauke ijiyan zuciya, runtse idanu yayi sosai yana rikeda ita sanan dakyar yace "zakisa kayanki"? Dawani irin sauri ta gyadamai kai, sakinta yayi ahankali yace "go" dawani irin sauri tafita daga jikinshi tasauka kasa duk yana kallonta baya tayi zata fadi sabida karfin dataji kafafunta basuda shi dawani irin sauri takama bango tahowa yayi bakin gadon da muryanshi dabata fita sosai yace "careful" gyadamai kai tayi sanan ta tsugunna tana tattaba kasa riganta ta lalubo dawani irin sauri tajuya tacire shimin shi ta ijiye tasaka rigan batare datama tsaya takan bin neman bra dinta da gyalenta ba ga gashinta daya gama haukata mata tai hanyar kofa dasauri zata bude, cikin kakkausar murya yace "Ke" dasauri ta tsaya tareda juyowa jikinta na bari tace "na'am Ya Asad" dariyan dayaji yazomai yarike yanadan cizan lips dinshi sabida azaban dayake sha na blue balls, ahankali yace "on the light" hannunta tasa abangon wajen tana yawo dashi kafin taji switch takunna dakin yay haske tasauke kanta kasa, jikinta yakasa daina rawa tana fidgeting, tundaga kan kafafunta yake kallo har zuwa kanta, gashin nan shi kanshi mamaki yayi to dambe yayi da gashin nata danshi kanshi baisan lokacin daya hargitsa mata kai hakaba zaka dauka mahaukaciya ya, gashin kaman buhu, wasu na baya har waist dinta, some na gefen fuska, some na tsaye kawai asama, ba dankwali ba hula ko takalmi batasa ba wai tafiya zatayi, ga Bra dinta dayake gani akasa batasaka ba kana ganin gaban riganta kasan ba bra ajikinta, pillow yajuya yadauka yadaura kan cinyanshi sabida tarufe abin dataki kwanciya sanan yasa hannunshi yadauki ribbon dinta dake kan gadon yace "come" ahankali ta taho jikinta na shaking ta tsaya agabanshi batare data kalleshi ba, hannunshi yasa yajawota sanan yazaunar da ita kan pillow daya ijiye kan cinyanshi, wani kalan ijiyan zuciya yaji tasauke na tsoro, kafin ahankali yasa hannunshi kan gashin yamata parking yana shakan kamshin da gashin keyi na turaren gashi ga gashin so soft kaman karya dena tabawa, da kyar shima yamata parking din yayi ba laifi amman dudda haka ba kaman na yanda mace zatayi ba, gyalenta yadauka ya rufe mata kan da kyau yasauke shi yana rufe mata kirjinta dashi yace "this should be the last time dazaki fita da this kind of veil" gyadamai kai tayi ahankali, murya chan kasa yace "go to the toilet and wash ur face saiki tafi" gyadamai kai tayi duk taki takalleshi ta tashi tabude bathroom dinshi wow bathroom dinshi yamafi dakinshi kyau gashi so neat, wanke fuskanta tayi tasa bakin gyalenta ta goge ruwan sanan tabude kofa tafito tsaye taganshi agaban kofan yasa gajeren wando amman gaban wandon amike sambal kaman yasaka wani itce aciki, dawani irin sauri ta runtse ido takasa fitowa ta tsaya chak awajen, ahankali yasa hannunshi yakamota yasata ajikinshi rungumeta yayi tsam tsam batare dayace mata komiba yanajin yanda gabanta ke faduwa, yakai kusan 3min ahaka sanan yacirota daga kirjinshi yay cupping face nata da hannayenshi biyu yana kallon fuskanta da yanda ta datse idanunta gam sanan yakai bakinshi goshinta ya manna mata kiss, murya chan kasan makoshi yace "feel free kigayama Ammi ko Grandma ko anybody komi" dasauri tashiga girgiza mai kai alamun bazata fadiba fuskanta nayi kaman zatai kuka, dan murmushi yayi yace "kuma fada, nima inada abin miki ai, leave my room mara kunya kawai" yay maganan yana sakinta da sauri hartana nema tafadi sabida sauri tawuce kofa juyowa yayi yabita da kallo budewa tayi tafita ta maida kofan tarufe, ahankali yajuya yadan daga labulen window ganin babu kowa a compound though akwai uban motoci yasa yasauke ijiyan zuciya, gani yayi tafito compound din dasaurinta daidai Sharif na bude gate yana shigowa dan awaje yay parking, ganinta yasa yakalleta cikeda mamaki yace "Du'a" murmushi takakalo tamai tace "ina kwana Ya Sharif" bama tajira amsan shiba tafice daga gidan harda dan gudun ta, dan ware ido yayi yace "ina kwana" saikuma yay shiru ganin motan Asad pake agaban flat dinsu, ga idanun yarinyar sunyi ja har sundan kumbura sabida kuka yasa kawai yacigaba da tafiya abinshi, sauke labulen yayi sanan yabude kofan bayi yashige abinshi ranshi fess. Ahankali tabude gate din gidansu da akai decorating ga kujeru ga abinci ga mutane ana hayaniya sabida akwatinta da aka kawo yasa tafito dasauri ta tsaya a kofar gidan ita bama tasan inda zataba, gajiya tayida tsayuwan ta shiga gidan kanta akasa tana tafiya kaman daga sama taji anja hannunta dasauri tajuyo Aneesah tagani hannunta daya daure a shoulder kaman wacce takarye kafinma alura dasu janta tayi suke shiga dakin security gidan dake musu gadi, suna shiga sukai zamansu akasa sabida shi yanachan tsakar gida, ahankali Du'a dake kallonta tace "maiya sameki a hannu" murmushi tayi tadauke kai dasauri tace "bakomi Anty Du'a" bude idanu Du'a tayi tana kallonta, hakan yasa tajuyo takalli Du'a tace "naga fitanki daga gidanmu, naga yanda kika shigo nan kika kuma fito daga window dakinmu nasama, shine nace bari nafito nasameki ina fitowa kina shiga ciki, ke bakisan ba'a ganin Amarya ba Allah yasa basu lurada ke ba, duk fa danginmu ne anan da yan uwan su Daddan mu, da kawayen Ammi, thank God basu ganki ba Anty Du'a, but how comes batare dasu Rahima kika fita ba"? Tama Du'a tambayan saikuma dasauri tai murmushi tace "ohh natuna maybe Ya Asad ne yadawo dake" tasake murmushi dakana gani kasan she's hurt, ahankali Du'a takama hannun nata tana kallo sosai fa ta karye, dan da igiya awuyanta ma take supporting hannun, ahankali tace "Aneesah what happen to your hand? Dama karyewa kikayi saisa ban ganki ba maisa babu wanda yafadi mini danazo na gaisheki kuma saida na tambaya ina kike, what happened?" Du'a tasake tambaya cikeda bala'in tausayinta, dan murmushi Aneesah tayi sanan ahankali tace "kwana na 5 a hospital ma" hawaye Du'a taji yazo mata tana kallonta sabida ta rame tai wani iri, kafin ahankali tace "Ya Asad ne, dagani harsu Zeezee da Billy" saikuma ta girgixa kanta dasauri tace "amman nima nasan nina jama kaina, nai laifi so I deserve his punishment" kallon Du'a tayi dataga hawaye yacika mata ido tace "kema is because I trust u please karki gayama kowa he made everything look like an accident" dan murmushi tayi takalli Du'a ahankali tace "Du'a Ya Asad na sonki sosai wlh" tai murmushi sanan tace "I thought kece kika kwacemin shi but after yanda yadawo dagani har kawayena, ba su Zeezee kadai ba har wayanda sukai chatting naki up suna zaginki yahada mu duka yaci ubammu sanan yasa mukai signing under taking if anything happens to you to sune, all my friends hate me now sunce nasasu a trouble da kullesu ma zaiyi kinga kukan damuka dinga yi sabida yanada evidence zamu iya zuwa gidan yari ko bamu jeba barin ma kawayena sunbata sunan gidansu, so da kyar yahakura fa, Ya Asad almost killed me sabida abinda namiki Du'a da ace baya sonki dabazai taba rama miki, yanzu bayamamin magana and yace zai karbi transfer later a school northwest zai maidani a kano yakomar dani gidan ubana, wai he don't wants me anywhere near you because I am toxic and ke bakisan komiba kar yazo watarana na kashe ki, har gidan nan shiya hanani shigowa ma" takashe maganan bakinta narawa sanan ahankali tace "Du'a please ki rokeshi karya komar dani wajen Babana, kinga Babana baida kudi kaman Dad, kuma a family mu Dad ne kawai mai kudi shike kula da kowa harda su Rahima da Ya Sharif da kakanmu Dadda dake kano da Mamana Anty Turai, shine komi namu, saikuma Ya Asad dashima yake bamu kudi sosai, wlh I cannot leave agidan mahaifina, kuma kowa yasani idan Ya Asad yace saiya maidani wlh ko Mamana Anty Turai bata isa tai wani abuba Ya Asad taurin kanshi yasa yafi karfin kowa har Dad shakkan shi yake, Du'a please nasan hala baki saniba wlh yana sonki kome kikacemai zaiyi, Du'a please Anty Du'a I am so sorry, kiyafemin, wlh wlh bazan kara miki abinda nayiba, all what I've said nafadi ne out of jealousy I didn't mean anything, Du'a please" ahankali Du'a ta rungume ta, dan ta bala'in bata tausayi, yanzu Asad muguntan shi yakai yaci uban sister shi, cousin dinshi, his blood haka? harda karyata, to ita waye dabazai iya mata sama da hakaba, tadade suna kuka sanan tadago hannunta takai tasharema Aneesah hawaye ahankali tace "Aneesah I am sorry kiyakuri please, dukni najamiki, I am sorry" sharemata hawaye itama Aneesah tayi tace "Anty Du'a stop telling me Sorry, ni yanzu kanwar kice, kece big brother wife dinmu" wani iri Du'a takeji ahankali tace "dan Allah kidena cemin Anty" makemata kafada Aneesah tayi tana tashi tsaye tace "bari natafi gida karki fito fa saisun tafi, zan fadama security kina nan" bata jira amsanta ba tafice, security dataga yana kokarin shigowa dakinshi tagayana Du'a na ciki sanan tafito daga gidan daidai Asad na fitowa a motanshi daga gidansu, chak ta kame awajen a tsaye tama kasa koda motsin kirki saida yazo daidai wajen sanan taga ya saukar da tinted glass dinshi kasa, wanan karan kananun kayane ajikinshi idanunshi sanye da bakin glasses ahankali yasa hannu yazare bakin glasses din yazuba mata mugayen idanunshi dayasa tafara shaking, bakinta narawa sosai tace "Ya Asad is not what u think wlh kallo naje nayi nakai akwatin, dan Allah kayakuri" wani irin kallo yamata wani mugun kalan wulakantaccen kallo dayasa saida taji hanjin cikinta yakara sanan yadauki glass dinshi yamaida a ido yamaida glass din motar sama sanan yaja motar, dasauri tajuya tashiga gidansu tanajin wani kalan bakin cikin dabata tabaji ba arayuwanta barinma na komarda ita Kanon dazaiyi_babu randa zatai salla dabazata roki Allah yasa ya hakura ba. 5️⃣9️⃣ DUK WACCE TAKARANTA LITTAFIN NAN BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA. THIS BOOK IS 500 PAY INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK SAIKI TUROMIN EVIDENCE OF PAYMENT TA WATSAPP NUMBER NA 07012181461. YOU CAN CHAT ME UP DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK wa.me/+2347012181461 Sai wajajen 6 aka waste daga gidan Grandma har kawayen ta duk suka tafi yan aiki ne kawai suka rage, kaga Grandma ko ubar Amarya albarka, kawo akwati kawai amman tayi gayu kaman adauketa, karan kiran sallan magrib yatada Du'a daga bacci datayi anan kasan dakin security, jin gidan yay shiru yasa ta tashi ahankali tabude kofa tafito tashiga ciki, taga aike aketayi gidan ya kacahme ga akwatuna ko'ina afalon su Razika nata aiki da matan dake mata gyaran jiki itama tana tayasu, ganinta yasa Grandma tajuyo tai wani murmushi tace "oyoyo taho nan yanaganki wani irin, zonan zazzabi kike ne" Grandma tajata jikinta cikeda so tana taba fuskanta da wuyanta jin na zafi yasa taji dadi tace "bacci kikayi ne" gyadamata kai tayi tace "eh adakin security a kasan falonshi nadawo gida yacika kuma banso a ganni" baki Grandma takama tace "shine bakisa ankirani na nema miki waje ki boye ba, oya wuce kitafi sama kiyi wanka kizo kisha magungunan ki amiki turare, gobe su Maman ki zasuzo, jibi za'a fara shagalin biki" gyadamatakai kawai tayi ahankali sanan tawuce sama, dakinta tabude tashiga ganin yawancin kayanta an kwashe barinma na amfanin ta yasa tafito ganin Grandma natahowa yasa tace "menene"? Ahankali tace "Grandma kayana ina suke"? Murmushi Grandma tayi tace "daga gobe a side dina zaki dinga kwana saisa nai clearing abubuwan dakike amfani dasu nakaisu chance, wanan da yan gidanku zasuzo I don't wanna take any chances wata ta takuraki ko aci zalunki, so u are staying with me all through, tafi kije kiyi wanka kizo" juyawa tayi tashiga dakin nata Grandma tabita da kallo sanan tawuce tana duba sauran dakunan sama datasa agyara sabida bakin dazasu fara zuwa ganin ko'ina fess fess har dakinda Asad ke zama yasa tafito takoma kasa wajen abincin Du'a. Bayi tashiga zata fara wanka saikuma ta tsaya tai shiru tanason tai wani tunani amman tunanin nabata kunyan yi, wankan tsarki nadaga cikin abubuwan data iya lokacin kafin ma a dena hanata fita, kuma lokacin data fara MP Mami takoya mata wanan, banda haka kwanan nan duk idan lesson Ustaz malamin ta yazo suna fiqihu yana fadamata dalilan dakesa ayi wankan tsarki ciki harda abinda Asad yamata dazu, runtse idanunta tayi taji wani kalan shock tuna abin kafin ahankali tai wankan, wanan uban gashin nata saida tajika, fitowa tayi daga wanka tadaura towel akirji tadaura karami akanta daidai Grandma na shigowa dakin dawani kopi da kula a hannunta, baki tasaki tace "keda za'ama gyaran gashi jibi maisa kika jika kanki" juyawa tayi tai wardrobe dinta tace "kaina ke ciwo" ijiye abincin Grandma tayi tace " bari naje nakawo miki panadol" kaya tasa sanan tai salla karfi tazo tazauna karfi dayaji Grandma ta sata agaba ta shanye abubuwan data kawo mata tass, tana zaune adaki an hanata komi daga anata magunguna sai azo amata wani abu wankan turare daga baya bacci yay awon gaba da ita. Tunda sassafe aka tashi agidan sai aikace aikace ake itako ko tsinke Grandma tahanata dagawa saima wani special gyaran jiki da akemata nasu dilka da turare, bayan angama wata waxing din dayasa tasha kuka dan saida Grandma ma ta tsaya akanta sanan tahakura, sai wajajen one aka gama komi aka mata wanka Grandma tadauko mata wata sabuwa English atampa cikin wanda tadinka mata milk mai shegen kyau da tsada tasata tasaka, shiryawa tayi ciki aka mata dauri dudda batai kwalliya ba but kana ganinta kaga Amarya to be, dakinta Grandma tawuce da ita tace "Hamad yakirani sun shigo Abuja wai" gyadama Grandma kai tayi ahankali jikinta duk yay sanyi, murmushi Grandma tayi tace "bari nabada nama akawo miki ko kyayi fara'a" murmushi tayi kuwa Grandma tai dariya tafice, tana kitchen tana kokarin debanma Du'a nama aka taji anbude gate, Razika dake kusada ita cikeda murna tace "Hajiya sune" murmushi Grandma tayi tabata naman tace "kaiwa Du'a kiga" sanan tawuce tafita da fara'anta, motoci uku ne, Sienna Abba ce agaba, sai wata karaman mota Honda, saikuma bus din Abba wacce Ya Hamad dake sanye da kayan sojoji keja, sosai Grandma ke murmushi tace "oyoyo oyoyo" yaran ne suka fara fitowa daga mota su Amra, Aneela, Mudasir, da Muhammad suna tahowa wajen Grandma da gudu suna kallon gidan, kafin Mum ta sauko taci wani hadadden atampa fuskar nan ba yabo ba fallasa, saiga Hawwa da Nana dasuka saka kaya iri daya sunyi kyau ba laifi sai kalle kalle suke, saiga Mami itama tadan rake but she is looking okay, sai Hamad daya sauko duk suka taho wajen Grandma, motar tsakiyan kuma wata matace tafito babba ce ba yarinya ba baka tana mika hannunta cikin mota saiga wata tsohuwa tukin tafito rikeda goro a hannunta tana tafiya adudduke ranta abace kana ganinta kasan wanan tsohuwa fitinanniyar tsohuwa ce, ga uban lalitan data daura, saikuma motan Abba wanda yake shine aciki sai kannenshi maza dasuke uwa daya uba daya guda biyu. Cikeda fara'a Grandma tai gaida dasu Mom da ba laifi basu nuna wani face ba itama ta amsa su, tana rungume su Nana da Hawwa, kana ganinta kaga classic woman sanan takalli Mami dake kallonta asanyaye tace "kaisu ciki daughter" sanan takarasa wajen Kaka cikeda barkwanci tace "kishiyata agidana Allah yakawomin gasasshiyar tsuntsuwa baki barin gidan nan sainasa mai gida ya danna miki saki" tai maganan tana kallon Hamad, hararanta Kaka tayi tace "inkin isa kisashi, kin rabani da jikata wanan ma zaki kwace min shine, nidai ki kaini daki inba sokike kafafuwata su tsinke ba nashayo wanan uban tafiyan" dariya Grandma tayi takalli diyarta data rike mata hannu dake kallon Grandma ganin hadaddiyar mata tace "barni nakaita ciki" takama hannun Kaka sanan takalli su Abba tace "Alhaji kushigo agaisa afalo wanan tsohuwan tagaji" hararanta Kaka tayi tace "dadin abin ban girmeki ba" kwashewa da dariya Hamad yayi tace "zakaci ubanka ne bakin soja kawai" falo suka shiga da already su Mom suna ciki, sun kasa boye kalle kallen dasuke, sunsha jin labari cewa Mami yar masu kudi ne but basusan kudin yakai haka ba, yanzu dama a irin wanan gidan Du'a take, lallai. Zama duk sukayi dayake falon da girma yaci kowa yaran sai wasa suke, Kaka na zama tace "ina Du'an take" murmushi Grandma tayi tace "zatazo ta gaida ku ku huta kusha ruwa tukkuna ansha tafiya" tai maganan daidai su Razika da Shema'u dasauran yaran suka shiga gabatar da ruwan gora da drinks dabama susan irinshi ba, saida suka gama sanan Grandma takalli Razika tace "Razika kira Du'a" gyadamata kai tayi tajuya tatafi sama. Duk suna zaune falo harda su Abba duk anyi shiru kaman kowa yakosa yaga Du'a ne, Du'a tafito ahankali kanta akasa tana gyara lullubin babban gyalen da Grandma tabata tasaka, ahankali take tafiya gabanta na faduwa takasa dagokai ta kallesu, daga Mom, Kaka, su Nana da Hawwa sun kasa yarda Du'a suke gani, har shi Ya Hamad ma, kasa rufe baki Kaka tayi tace "jama'a yarinyar nan ce dai wanan koba ita bace"? Hamad dake gefenta yace "Du'a ce Kakus" cikeda masifa tace "yoni wai wagga Y'a kara komawa aljanna take kome" batare da Grandma takalleta ba tace "yarinya tai kyau dai Masha Allah maihadinta da aljanna" daidai Du'a takarasa saukowa, ahankali ta shigo falon takasa kallonsu tsugunnawa tayi atsakiyan falon tana wasa da yatsunta murya chan kasa tace "Abba ina yini, Baffa sannu da zuwa, Kaka ina yini, Inna ina yini, Mom sannu dazuwa, Mami ina yini, Ya Hamad, Ya Nana, Ya Hawwa ina yini, Aneela, Amra, Mudasir and Muhammad welcome" duk maganan nan tayishi ahankali cikin xakin muryanta dayasa jikake dakin yay tsit. Ahankali Abba dake kallonta yace "Du'a" sai alokacin tadago kanta takalleshi, hannu yamika mata, ahankali ta taso hannunta tasaka kan nashi zaunarda ita gefen kafanshi yayi yana kallon fuskanta yace "how are you Du'a? Ya shirye shirye"? Dan murmushi tayi tana kallon Abban nata ganin yau yamata magana faram faram ahankali tace "Alhamdulillah Abba" hannunshi yakai ahankali yadaura asaman kanta yace "Allah yamiki albarka, Allah yakaimu jibi lpy akaiki dakinki, Allah ya sanyama aurenki albarka" ahankali tace "Ameen Abba" wani irin murmushi Grandma tayi sometimrs rashin wayon Du'a pays her alot, kannin Abba dake kusada ita addu'a suka mata sanan babban cikinsu maibin Abba yace "saiki sanar da mijin naki iyayenki sunzo yazo yagaidamu anjima da daddare, yaga yan uwanki muna muganshi musan wanda muka bama yarmu, ayi zumunci" gyadamai kai tayi, sanan Abba yatashi yace "kutashi mutafi masallaci" tashi mazan Saukayi harda Hamad suka fice dan zuwa mosque. 6️⃣0️⃣ MASU FITAR DA NOVEL DINAN WAJE KUNMA KANKU MARASA AMANA. PAY 500 INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK SAIKI TUROMIN EVIDENCE OF PAYMENT TA WATSAPP NUMBER NA 07012181461 SAINAI ADDING NAKI A GROUP DIN DANAKE POSTING. CHAT ME UP DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK wa.me/+2347012181461 Kaka data kasa daina kallon Du'a ne tace "taho nan naganki yarinyar nan" ahankali Du'a tadago kanta Grandma takalla danko kadan jininta bai hadu dana kakarta ba, gyadamata kai Grandma tayi alamun taje hakan yasa ahankali tamike tsaye taje wajenta ahankali tazauna akasa, hanci Kaka taja agaban kowa jin wani hadadden kamshi da Du'a keyi tace "banda kyau har kamshin fata Allah yabaki ne, lallai nidai Allah ma yasani haryau nakasa yarda ke diyar Muhammadu ce billahillazi" Kaka tai maganan tana kama hannun nata tarike sanan tace "Ya sunan mijin naki" ahankali murya chan kasa tace "Asad" gyadakai Kaka tayi tace "tabbas haka Muhammad Muhammadu ko yafadi mini, dana aiko adaukoki akawomin ke chan Ikara ki zauna dani shine kikace ke aure kikeso, shikuma dayake uban naku wani zubin bakai gareshi ba sai ko ya aurar dake, ai shikenan tunda auren kika zaba, nidai addu'ata Allah yasa karya gano kinada jinin ifiritu ajikinki yasakoki tunda mun samu kin sami miji kin aure" daidai nan Grandma tace "kinga Kaka jikata batada jinin ifiritu jinin danki gareta, kumama bakisan wani abuba, Kakan Babana usulin shi balaraben Egypt ne, yazo naijeriya yay aure, to daganan ne abin yatafi muka duk aka haifomu bakake sabida matayen dasuka aura, Du'a tadauko jinin dangin ne na kakanni" baki Kaka tabude ganin Grandma na taran mata numfashi idan tana magana hakan yasa tahadiye sauran maganan tace "asheee" murmushi Grandma tayi tace "eh wlh, yanzu dai kugamacin abinci ayi salla saimu tafi sama kuga akwati" takalli Mom daketa kallon Du'a dake wasa da yatsunta tace "akwai wani abu dakike bukata akawo miki Maman Hamad" murmushin yake Mom tayi tace "a'a wlh" lafiyayyen abinci aka kawo musu daban daban ga namomi zuku zuku, bawai basacin abinci agidansu bane amman kaga wani abincin sai agidan wane da wane ga gasasshiyar rago, dayan flat din da Grandma tasa aka gyarama su Abba suna dawowa wajen aka kaisu dan su saki sanan aka kaimusu nasu abincin, zuzzuba abincin akayi sanan Grandma takalli Du'a tace "oya tashi kici abinci tareda yan uwanki" tanuna mata su Hawwa dasuka zubo abincin su a plate tare, gyadamata kai tayi tai wajen atsakiyansu tazauna ahankali sanan takalli Nana dake kallonta ahankali tace "Ya Nana" dan murmushi tamata tace "Du'a ya kike"? murmushi tayi tace "lpy lau" sanan takalli Hawwa dake kallonta tace "Ya Hawwa" murmushi taga Hawwa tamata tace "Amarya Du'a" dan murmushi tayi sanan tadau spoon dinta sukahau cin abincin bini bini Mami na satan kallon Du'a da tuni Grandma ta lurada ita kuma tasan bakomi take kallo ba illa girma dakuma kyau da Du'a takara, saida sukaci suka koshi sanan Du'a takallesu tace "kutashi muje dakina kuyi wanka ku shirya" basuyi musu ba suka bita sukai sama duk aka bisu da kallo, akwatinan dasuka gani afalon sama sukabi da kallo kusan set 15, sanan suka shiga dakinta shima kallon dakin suka shiga yi, skirt Hawwa tacire tai bayi dagudu tace "zanyi fitsari wayyo karya zubo" murmushi Du'a tayi sanan takoma kan gadonta tazauna, ahankali taga Nana tazo tazauna kusada ita hakan yasa tadan dago kanta ta kalleta hada idanu sukayi, murmushi Du'a takarayi tasaukar da kanta kasa, ahankali Nana takira sunanta."Du'a" dasauri tadago kanta takalleta, hannun Du'a Nana takama tace "nadade ina neman hanyan dazan kiraki nabaki hakuri, I am very sorry Du'a akan duk abubuwan danamiki akan Muhsin, Muhsin is nothing but a jerk nima daga baya nagane haka, bake kadai yabi ba, infact namaji dadi abinda yafaru badadan keba da yanzu na aureshi ina cikin bakin ciki, kece sanadin dayasa Nagano wayeshi, ashe duka friends dina na school daya sani duk yana dating nasu, mayen mata ne na karshe kuma dan iska, I was so blind by his love bangane hakan ba, kiyakuri kinji Du'a" Gyadamata kai Du'a tayi ahankali tana murmushi, Nana tace "bayan Ya Hamad yadawo daga kawoki Abuja yafadima Abba komi, saiya yakulle Uwani, Mai gadi dashi Muhsin din a police station, akayi case sosai sanan aka bashi hakuri yasakesu da sharadin ko akofar gidanshi yasake ganin any one of them hukuma zasu raba shi dasu ahaka case din yakare" gyadamata kai Du'a tayi daidai Hawwa tafito, tashi Nana tayi tashiga bathroom din, Hawwa takalli Du'a tace "kin kara kyau yarinyar nan, yaushe rabon damuyi fada" dan murmushi Du'a tayi tana mamakin yanda duk suka chanza toko sun kara hankali ne oho, salla sukayi sukahau bama Du'a labarin kano daga tai murmushi saita gyadamusu kai, kwala musu kira da Mom tayi yasa suka fita banda Du'a datai zamanta, duk afalon saman suka taru ana bude kayan Du'a dababu na Nigeria ko daya, daga akwatin har atampopin dakomi ma, Mom duk yanda taso kasa boye bakin cikinta tayi, harsaida Kaka yar bala'i tace "kekuma kowa na tofa addu'a bazaki tofa ba" murmushin yake Mom tayi dan daga ganin akwatin wani mai kudin Abuja Du'a zata aura, itada ta dauka wani mai gadi ne kokuma lebura haka zata aura, amman wanan akwatuna haka set 15, kowani saiti nada 3 dan designers akwati ne ba irin na Nigeria ba, ahankali tace "Kaka yarinya tai goshi Allah sanya alheri" da karfi Grandma tace "Ameen" sanan tanuna ma kowa dakinshi asaman dan suje suyi wanka su huta, kowa yatafi, su Hawwa suka koma dakin Du'a duk suna mamakin akwatin Du'a dan basu saba ganin irinshi a kano ba. Dakin Grandma Mami ta shiga, waje tasamu kusada Grandma tace "Mama Yaya Muhammad yace jibi zasu shigo ko ranan jumma'a" murmushi Grandma tamata tace "ashe kunyi waya haka yagayamin" shiru Mami tayi tana kallon mahaifiyar nata tasan har yanzu fushi takeda ita, ahankali tace "Mama dan Allah kiyakuri kiyafemin komi dan Allah" juyowa Grandma tayi takalleta kaman tai shiru saikuma tace "naso namiki yanda kikama Du'a yarki ne, nima na nuna miki baki da amfani kaman yanda kika nunama yarki, but I guess bazan iyaba Zainab" sauka Mami tayi daga kan gadon, guiwanta tasauke akasa tana kallon mahaifiyar tata, ahankali tace "dan Allah kiyakuri kiyafeni" hannu Grandma tasa tadagata dan tanason yarta bakadan ba, zaubarda ita kusada ita tayi tace "Na yafemiki komi ya riga yawuce Du'a tariga tai aurenta, ranan lahadi war haka ai tanama gidan mijinta so bakomi, yanzu dai akwai magungunan ta wajen Jummai, kinsan zan shiga hayaniya ba lallai nasa idoba kisamata ido makesure tashanye komi sanan taci abinci dan bata iyacin abinci har yanzu, akwai turaruka ma anan zaku dinga mata" gyadama Grandma kai tayi tace "to Mama" ahankali Grandma tace "kinga yaron daya wahala shi Allah yake kyautatamawa akarshen sabida ya wahala yay hakuri, Allah yabama Du'a miji, idan kinga yanda yaron kesonta dudda yana kokarin boyewa sai kinyi mamaki, ko bani duniya ayau Zainab na yarda da Asad zai kulada Du'a kaman kanwarshi wanan shaidar nimishi ita" murmushi Mami tayi hankalinta nakara kwanciya tace "Alhamdulillah". Wuraren 4 Dad yakira Asad dabayanan awaya, bai daukaba akaro na biyune yadauka, Dad yace "kana office ne" cikin muryan nan nashi na baison magana yace "ganinan zan shigo gida" katse wayan yayi yashigo yay parking sanan yafito yana kara kallon yanda ake aikace aikace ana decorating gidan for event sanan yay falonsu, Dad yagani zaune da kowa afalon ga wasu kwalaye sweet, goro tabarma da sauransu akasa duk ana magana, ganinshi yasa akai shiru yaran duk suka gaidashi, karasawa yayi yazauna kusada Sharif ahankali yana yatsine fuska danyagaji, harara Anty Turai ta watsamai, murya chan kasa yace "Dad gani" murmushi Dad yayi yace "My Son the latest ango, anyway family din wife dinka gabaki dayansu sunzo suna around, mahaifinta da kannen mahaifinta maza biyu, da macen, sai matanshi biyu da Maman Du'a da kishiyar, dakuma duka yaransu, da mahaifiyar Babanta Kaka su, inaso dakai da Sharif dawani abokinka ku shirya bayan magrib kaje kai gaisuwan iyaye ka gaidasu sanan kutafi da all this, bayan sallan isha'i mahaifinta da kannensu wai zasu tafi masaukin su, nayi nayi dasu su kwana tunda sunada nasu flat din, amman yace bazai iya kwana agidan suruka ba, so ku shirya karka bata musu lokaci kaji" gyadamai kai yayi, Sharif yace "tashi muje mu shirya, nama riga nakira Jabir" yatsine fuska yayi yatashi, Rahima nawani dan murmushi tana mamakin Asad kaga yanda yakeyi ne kaman ana tursasashi Ammi sai kallonshi take da tsoro karyace yafasa saisa wani sabon lallabashi take kwanan nan Allah sarki Ammi batasan danta yafi kowa son bikin nan ba. Flat dinsu suka shiga fadawa kan kujera Asad yayi ya kwanta yana lumshe ido, baki Sharif yabude yace "kasan karfe nawa kuwa katashi muje mu shirya" hararanshi Asad yayi yace "ko sarakai ne suka zo wlh sainai bacci na natashi I am tired" yay maganan yana lumshe idanu, girgiza kai Sharif yayi kawai yawuce dakinshi, kayansu da ya dinko dan shine Ammi tabama ragamar dinka all kayan Asad na biki yaciro wai hadadden ash din gizna da akamai riga da wando rigan har guiwanshi dawata bugaggiyar hula tambari daya shiga da shaddan, da sabon takalmi na Tom Ford da agogo dawasu sababbin turaruka yabufe dakinshi yabijiyemai komi akan gado sanan yawuce yakoma dakinshi yana kara kiran Jabir daya cemai gashinan a estate dinsu, shigowa gidan Jabir yayi sanye da kayan asibiti ajikinshi parking yayi yafito yawuce side din su Asad, ganin Asad kwance yana bacci yasa baiyi wata wataba yadaka mai duka abaya, tashi zaune Asad yayi dasauri yana shafa bayanshi hararanshi Jabir yayi yace "mune angwayen dazamu rigaka shiryawa, dalla Malam wuce muje kai wanka" dan gajeren tsaki Asad yaja cikeda kulewa yatashi ahankali yana gaba Jabir na biyedashi sukai sama yanaji yana gani suka sashi yay wanka, shegen wankan nashi ma saida yasa sukai missing magrib a mosque yana fitowa sukai jam'i anan falon sama sanan suka shiga saka kaya, Asad kadaine yasa ash shadda da Jabir da Sharif wasu fararen hadaddun yadi sukasa, fitowa Asad yayi ya shirya tsaf, koshi Sharif daya kalleshi saida yakara kallonshi rabon dayaga Asad da hula akai harya manta, guda yafara yace "wooo ango saura 2days da kacal" tafi sukayi shida Jabir suna dariya, Asad yace "wlh zance nafasa zuwa" yakuri kumuje inji Jabir, saukowa sukayi saida suka fara shiga wajen su Ammi, kasa daina murmushi Ammi tayi dataga danta saiya mata kaman ba Asad dinta ba, yanda suke kallonshi yasa yawani juya cikeda bori yace "kokuzo muje kona fasa zuwa" dasauri Dad yace "kunga kuwa ce kutafi Dr, za'a biyoku da kayan yanzu kafin dan borin nan yafara" dasauri suka bishi su Rahima sai dariya suke dannewa. A compound suka sameshi tsaye yana daddanna waya, hannunshi Sharif yakama yace "stop being anxious jor let's go" ko kulashi baiyiba ba suka fice, dayake anriga ansan da zuwan su an gyara gidan tsaf tsaf, Hamad ne yafito ya taresu yana kallon Asad da kallo daya yamai yagane shine mijin sabida yanda yafi dukansu haduwa, hannu yabasu sukai musabaha sanan yace "bismillah" yay gaba suna biyedashi abaya, gidan Grandma gidane daya saba zuwa amman yau sai gidan yamai daban, suna shiga falon Kaka ta kece dawani lafiyayyen guda kaman ba tsohuwaba, kowa na falon kallonsu suke barinma Mom dasu Nana dan basu taba tunanin mijin yahadu hakaba, awani sabon ruug da aka shimfida afalon suka zauna cikeda girmamawa, cikeda natsuwa sukai gaisuwa, amsasu Abba da kannenshi sukayi kafin anatsu dakin yay shiru, sanan ahankali Abba yace "Asad" dago kanshi ahankali Asad yayi, Abba yace "nasan banda ni da mahaifiyar Du'a babu wanda kasani anan, gabaki dayan wajen nan dakake gani yan uwan matan ka ne bari nafara da kainena Baffofin ta" sanan yanuna gefenshi yace "wanan shine Mustapha mai bina kenan da Auwallu, dagashi sai Aisha damuke kira da lami gatachan" yanunamai matar dake kusada Kaka tana murmushi tana kallon su Asad din taga hadaddun yan gayu, sanan yanuna Kaka yace "wanan itace mahaifiyata, Hajiya Kaka" washe baki Kaka tayi tanacin goro, sanan yanuna Mom yace "itace mata ta tafarko, mahaifiyar Hamad, Nana, Hawwa, Amra, da Amira duk gasunan" yanuna su gabaki daya, sanan yanuna Aneela dake kallon Asad din yace "ga kanwar Du'a dake binta, Du'a ce tafarko awajen mahaifiyar ta sai Aneela, sai mazan nan Mudasir da Muhammad" dukansu kallonsu Asad dake to some extent baiyi blaming illiterate tsohuwan chan dake kiran Du'a da mayya ne ko whatever like idan kaga this whole family zaka rantse ka kara rantsewa sanan ka kara rantsewa ba daga gidan Du'a tafito ba, babu tawani abu da Du'a tai using tai kama dasu, da ita dasu kaman gabas ne da kudu, gabaki dayan family bakake ne, black beauties suna kyau masha Allah, ga yaran bakutaye kaman Du'a dan itama ba wata siririya bace, amman dai sun fita kiba but still ko kadan Du'a batai kama dasu ba". Sosai Hawwa ke kallon Jabir daya mata kyau sosai har saida suka hada ido dasauri tadauke kai, fada aka musu kannin Abba suka bashi shawarwari na rayuwan aure, bayan sungama Kaka tace "sanan karike zikiri sosai, wanan da bamusan tsatson taba karkayi bakin dare" wani mugun kallo Abba yamata dayasa taharareshi ta fito da goronta ta balla tai shiru, saida aka kira isha'i sanan suka tashi kudi suka ciro mai yawa suka ijiye akasa Abba zaiyi Magana Kaka tawani zabura tamike hartana take kafan Mom takwashi kudin tana shimusu albarka, girgixa kai kawai Abba yayi yama kasa magana suka wuce suka fita har gate tarakasu Kaka na godiya sanan aka shiga shigoda tabarmai da kwallayen sweet dinda suka kawo. Mom kaman zata mutu wanan hadadden mijin da Du'a tasamu bashine wanda tagani kwanakin baya a TV ba ana hira dashi, wanan yaci uwar Muhsin a kudi da kyau dakomima, wayyo Allah na tafadi zuciyanta namata zafi. 6️⃣1️⃣ DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFI BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA. chat me up directly by clicking on this link wa.me/+2347012181461 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 08133079957 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 or 08133079957 call or Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 08133079957 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Bayan Sallan Isha'i su Abba suka musu sallama suka tafi. Grandma bataji kunyan kowa ba wuraren 10 ta kwalama Du'a jira agaban su Mom da Kaka dake falon sama tace "Du'a oya zokisha magani ki kwanta" fitowa tayi daga dakinta inda su Nana suke sanan ta taho dakin Grandma din, Kaka ta ballama Grandma harara, saida tabata magungunan dare sanan tasa taje tayo wanka sanan ta kwanta akan gado sai bacci daman tagaji batai na rana ba yau, Grandma kuma tafice taje tasame su a falo tashiga hiransu, ahankali Mami tazame ta taho dakin Grandma, zama tayi ahankali abakin gado tana kallon Du'a din dake bacci, tadade tana kallonta kafin ahankali takai hannunta tadaura asaman kanta tana shafawa kaman ta tasheta ta rungumeta takeji. Washe gari da sassafe aka tadata aka mata turare dawasu abubuwa dabatasan na meba kafin mutane su cika gidan, danyau za'ai wankin Amarya, gobe jumma'a Asa lalle da yamma walima, sanan jibi asabar jinin biki dakai amarya ahakama dan shege Asad yace shi bayason wani event yace musu ko sunyi bazaije ba kuma sunsan zai aika saisa basuyiba dan Sharif yazo yahada dinner. Wuraren 9 Abba da kannenshi sukazo gidan dawata katuwar trailer na kayan daki, Grandma tai mamaki bata taba sanin zai mata kayan dakiba dan tuni tamata komi, some of kayan dakinta ma Muhammad danta dukya turosu daga UK but dudda haka bazata taba hana Du'a kayan da mahaifinta yamata ba, Sharif takira yahada trailer da security aka tafi da kayan gidan Du'a, Grandma ta aika trusted friends dinta da some yan aikin data kwaso aje gidan a jera kayan tama Abba godiya da kannenshi suka tafi. Wuraren 2 na rana aka fara event din ana kidan kwarya, Mami dakanta da shirya Du'a cikin wani hadadden lafaya, da kyar ta iya hadiye kukan datakeji she can't believe yarta tai aure bikin ta ake, ita Du'a din tai zuru zuru tana neman fara kuka kaman yau za'a kaita komi wani iri yamata, aka fita da ita tsakar gida su Rahima duk sukazo suna kallon yanda ake wankin Amarya ana waka suna amshi suna rawa the event was fun sai wuraren 5 aka gama, dakinta Grandma takaita dan tai wanka taci abinci tasha magani tahuta tai bacci haka akayi kuma. washe gari sa lalle shi dj aka kira akai decorating compound din, ga masu lalle sama da 30, ja, baki duk wanda kikeso za'a miki, sanan ga Ogan masu lallen da ita ce zatama amarya kadai, fitoda Du'a akayi cikin wata vilisco atampa red worth 200k ana rawa sanan Mami ta zaunar da ita akan filo dj yasaki kida aka fara rawa ana mata lalle gidan yacika makil, ihu Rahima data fita waje tayi tace "agyara ga ango zai shigo yabiya kudin lalle" gyarawa akayi, Mom dake tareda wasu kawayen ta data gayyato yan Abuja duk suka zubama gate idanu, Sharif ne yafara shigowa cikin manyan kaya, saiga Asad yaci wani mahaukacin faran shadda yasa bakin glass a idanunshi fuskar nan nashi bayabo ba fallasa yay kyau sosai, saiga wasu abokanansu guda biyu suka shigo Dj nasaki wani sabon kida. Ahankali Asad ya tsaya agaban Du'a da aka gama zanama lallen hannu daya hadu sosai yana kallonta ta cikin glass, dudda kanta akasa amman tai bala'in kyau, hannunshi yasa ahankali yazare glass din yamikama Sharif dake gefenshi yana wani irin kallonta cikeda so, sanan yatura hannunshi a aljihun riganshi yaciro wrap na yan 1k sababbi guda biyar, ahankali yace "Du'a" dago fuskanta tayi ahankali takalleshi, wani dan lumshe ido yayi yabude kafin ahankali ya ijiye mata wrap din kudin ajikinta daya bayan daya, sanan yakara sa hannunshi a dayan aljihu yaciro 5 more ya ijiye mata, sanan yamikama Sharif hannunshi batare daya kalleshi ba, dasauri Sharif yaciro 5more yabashi sake zuba mata yayi, sanan yasake niko hannu aka sama 5 again yasake zuba mata, saida ya ijiye miliyan biyar duk Mom na kirgawa sanan suka wuce suka tafi ana mugun ihu, sai wuraren 4 aka gama sanan taje tai wanka lallen yamata kyau ja da baki abinku da amarya sanan aka shiryata cikin wani leaur abaya akazo walima sosai tai kuka dan waazin ya ratsa jikinta gani take mafarki take, dan she can't believe itace ke aure Amarya, duk wanan jama'an datake gani sabida itane sukazo wajen nan ga Grandma da mutane wai ahaka ma dan gobe asalin ranan biki batayiba danhar ministers ta gayyata. Ance rana bata karya ko, yau asabar ranan biki, gabaki daya Du'a farkawa tayi kaman ma batada lpy, kana ganin fuskanta kaga fuskan wacce jira kawai take ko murmushi ne kamata tafashe da kuka, gashi tayi wani arnen kyau tai fresh, yau magungunan da kalan wankan turaren da aka mata daban ne, biyonce makeup artist aka dauko tamata makeup ta shirya cikin wani white gown aka gyara gashinta da Solange tamata akai parking aka mata dauri da head dinta aka zubo da gashinta ta tsakiyan ashoki, subhanallah, yau duk kunyan Mami dataga yarta rungumeta tayi sai kawai tahau kuka, shigowa Asad yayi shida friends cikin shadda da za'ayi couples pictures photo shoot, duk iskancin shi da boye abinshi saida ya rungume matarshi agaban kowa yana ganinta su Rahima sukahau ihu, Mami kuma tashiga daki kunyan siriki, sanan ahankali yariketa yamanna mata peck a forehead aka dauki hoton, kana ganin Asad kaga akwai wani special happiness dayakeji na musamman yau, kusan 2hrs akayi ana hotunan sanan suka sake mata manni shida abokanshi tunda ba dinner zokaga kudi afalon Grandma harda dollars dan da Asad da Yayan Mami da matarshi dasukazo jiya da daddare dukda dollars suka mata manni, Mom da yaranta sai suka dawo yan kallo. Sha'aini akayi nagani nafadi manyan mata na minitoci da ministers duk sunzo bikin manya gidaje biyun nan sun cika makil, tun around 1 Du'a tafara kuka sabida yanda duk wanda zaizo fada ake mata akan zaman aure, gabaki daya batada joy tai zuru zuru tai wani shegen kyau kuma. Wuraren 5 sabida Asad ja'irin yaro ne mara kunya motocin abokanenshi sukai layi kofar gidan Grandma wai sunzo daukan Amarya, da Ammi taji labarin salati tahauyi tace "jama'a yau naga da, wai Asad harya tura motoci yo saikace wani gari za'a kai Amarya" Wani sabon wanka Grandma tasa Mami tamata na turare bayan tai sallan magrib sanan aka kawo wani lafiyayyen lafaya aka sama ta sarkan gold aka shiryata tsaf aka lullube mata fuska sanan Mami tafito da ita aka kaita wajen Kaka fada tamata sosai sanan tace dare yayi tagaji amman gobe zatazo yaduba gidan nata, sanan aka kaita wajen Abba da kannenshi fada suka mata sosai dayasa tasha kuka sosai, fitoda ita akayi ana waka ana rawa aka kaita gidan yan uwan mijin, Ammi rungumeta tayi sanan tamata kyauta na darham dubu daya suma ne kawai Mom batayiba sanan aka mata wazai, Ammi tasa tai sallan isha'i sanan aka fito da ita, akofar gidansu taga Grandma tsaye tana magana dasu Sharif dawani irin sauri ta fizge hannunta Grandma jitayi anririketa ana kuka sosai, tace "Grandma dan Allah ni awajan ki zan zauna please Grandma, dan Allah bazan ba" duk dauriyan irin na Grandma saida tadan koka rungumeta tayi sosai tana mata wasu maganganu akunne, sanan takaita tasata amota tarufe sosai Du'a ke kuka kaman zata mutu, Grandma ma Hawaye ta shirya tana tsaye aka wuce da Du'a amota zuwa gidan mijinta, Kaka da Mami ne kawai basu bitaba ita Kaka gajiya ce dan dataje, amman Su Mom da Nana duk sun bisu. Wani anguwa sukayi acikin Asokoro District, anguwan shiru babu hayaniya gaban wani dankareren gida da ita kanta Mom gani tayi yafi na Grandma da gidan iyayen mijin dayake Minister ma kyau, wani security mai uniform ne yabude gate din motoci suka shiga, Allahumma Barik! Mom taji Nana dake kusada ita tafadi sabida haduwa gidan, parking aka yiyyi suka fito, Babban kanwar Grandma da Grandma ta damka mata amanan Du'a da matar Muhammad Yayan Mami ne suka fitoda Du'a daga mota kanta na kasa, gasu Rahima da Mariya banda Aneesah, gawasu yan uwa, da kanwar Su Abba itama sai kalle kalle take baki yaki rufuwa ana rawa ana wakokin kawo amarya bismilla akasa tayi sanan tashiga gidanta da kafan dama jama'a suka bita, wani irin mad penthouse ne gidan, ya ilahi! bene biyu ne dana farkon falonta, sama nabiyun nashi, bango Mom tadafa jin tana nema tasume to kodai mijin ne suka mata kayan dakin nan! Dudda su Mami nada kudi ina uwarta taga irin wanan kudin, nan ko batasan Muhammad da Grandma ne suka mata komi ba, kayan da Abba ma yamata a guest house aka dankasu kayan kitchen ne aka debo aka kawo aka danki dasu a store dinta, kuma Abba yay kokari yamata set na gado da kujera guda daya daya masu kyau sai kayan kitchen. sama aka kaita tana wani irin kuka sanan aka zaunar da ita akan lafiyayyen gadonta, wani kunu da Grandma tabama kawarta a flask cewa ana zuwa abata tabude tace "gashi shanye Du'a Grandma dinki tace na makesure kinsha, please kidena kuka idanunki sun kumbura dayawa" gyadamata kai tayi sanan takarbi flask din takai baki, itadai batasan kynun me wanan ba amman all abinda takeji is dabino, kwakwa, dakuma abu kaman yogurt kunun dai dadi, kira yaran duka sukayi wajen dakin suje suga gida, ga gidan kamshin turaren wuta sanan da kanwar Abban ta, da kawar Grandma da Matar Baffa Muhammad, da Mom dake wajen dabata cewa komi suka shiga yimata fada sosai ana mata nasiha mai ratsa jiki, kaga Du'a saita baka tausayi, wuraren 10 abokanen ango dake jiransu awaje suka keko sukace munzo tafiya da manya, baki Kanwar Abba takama tana murmushi tace "Baza abarmu mu kwana ba ai shikenan, kumuje su Nana sa zauna ayi siyan baki kafin adawo dasu" sosai Du'a tahau kuka saukowa tayi daga gadon zata bisu amman suka sake maidata suna bata hakuri sanan suka tafi, su Nana suka shigo dakin, zama kusada ita Mariya da Rahima sukayi, Rahima tace "common Du'a kukan ya isa haka idanunki sun kumbura" make mata kafada tayi tana kuka kaman wata baby tace "ni wajen Grandma zan koma" kallon junansu sukayi harda su Nana sanan dukansu suka kwashe da dariya Du'a takara fashewa da kuka, zasuyi magana sukaji anyi sallama, dasauri kowacce ta gyara, Rahima tace "anzo siyan baki ba mutunci, idan basu bamu 10M ba bazasu ga Amarya ba" zaro idanu Nana tayi jin yanda ake kiran kudi, Rahima da mariya suka tashi sanan suka kalli su Nana ganin sun zauna yasa tace "kutaso muje" tashi sukayi suka bisu kasa, wasu hadaddun classic men ne gayun abuja afalon a zazzaune harda Asad dake sanye da wata white shadda yakafa hula yay wani irin bala'in kyau yana daddanna wayanshi, kana ganinshi zakasan shine angon but yanda yakeyi bazaka dauka shine angon ba, yana zaune yana jinsu Rahima tadage aiko saida takarbi 10M din sanan tace "bari nakawo muku Amarya" "Ke" sai alokacin Asad yay magana, duk kallonshi akayi harsu Nana, kofa yanuna mata yace "kuwuce kubarmin gidana I am sleepy" kafin ma Rahima tai magana abokinshi su Jabir sukahau mahaukacin ihun shakiyanci afalon, Sharif ma murmushi kawai yayi yatashi yace "kunga kutashi muje mu sauke yaran nan mutafiyan mu tunda mu dan iskan nan yake kora, don't worry mumadai mun kusa shiga daga ciki" yatsine fuska yayi kaman bada shi akeba yadanyi murmushi kadan yacigaba da danna wayanshi, yana zaune awajen duk suka fice, saida yaji karan motansu da fitansu da rufe gate din sanan yatashi ahankali, rufe kofan falon yayi da key sanan yawuce kitchen wani hadadden warmer yabude yadau plate yaciro wani grilled chicken yasa a plate da fork sanan yadauka a tray yafito daga kitchen din yay sama, dayazo falon farko saida yaji sound na kukanta tsayawa yayi yana sauraron yanda take kuka ahankali tana kiran sunan Grandma sanan yawuce saman shi, gawani irin mad palour awajen da akamai wani design aka zuba wasu beds kujeru awajen da complete wall TV, falon anyishi kaman cinema, wani daki yabude Ya Rabb! dakin komi is off white gadon ciki zaka dauka gadon sarki ne, ijiye tray yayi kan lallausan carpet din wajen sanan yabude kofa yafito yasauka, ahankali yabude kofar dakinta da sallama abakinshi, dago kanta da sauri tayi takalleshi gabanta nafaduwa, hada idanu sukayi ahankali tasa bayan hannunta dayasha lalle ta g0ge fuskanta lips dinta narawa. 6️⃣2️⃣ DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFI BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA PAY 500 INTO 3107021073 AISHA MUHAMMAD FIRST BANK SAIKI TUROMIN EVIDENCE OF PAYMENT TA WATSAPP NUMBER NA 07012181461 YOU CAN ALSO CHAT ME UP DIRECTLY BY CLICKING ON THIS LINK wa.me/+2347012181461 Maida kofan yayi ahankali ya rufe sanan yakaraso cikin dakin gaban gadon ya tsaya daidai inda take yana kallonta, murya chan kasa yace "why are you crying" girgixa mai kai tayi batare datai magana ba kaman yar baby, hannunshi yamika mata, kallon fuskanshi tayi da jajayen idanunta sanan takalli hannun ahankali Akuma tsorace tasa nata hannun acikin nashi, hannunta dumi gashi duk ruwa sabida yanda taketa goge hawayen dashi, lallen hannun dayamai bala'in kyau yabida kallo kafin gently yasa yakai dayan hannunshi yakamo dayan hannun nata sanan yadauketa yasauko da ita dagakan gadon, kawai jitayi ya rungumeta tsam tsam murya chan kasa yace "Assalamu Alaykum Mrs Asad Abdullahi Kitse" sanan ahankali yacirota daga jikinshi yay cupping face nata da two hands kafin gently yakawo fuskanshi saitai fuskanta, dawani irin gudu ta runtse idanunta tadauka wani abun zai mata ahankali ya manna mata very light kiss a forehead, sanan yajanye bakinshi ahankali kaman baiso yacire shi kanshi kamshin datake na gyaran jikin amare dana wankan turare datake yana wani dibanshi he's just feeling kaman ya kankameta and never let go of her, sanan yakama hannunta yafara tafiya ahankali tana biyedashi abaya, bathroom dinta yabude ya shiga, karamin tap yabude mata sannan yawani jawota ahankali yasata agabanshi yana kallon fuskanta ta mirror dake gabansu dabama ta luradashi ba, sanan yakai hannun karkashin tap din ruwa na sauka kan hannun murya chan ciki yace "perform alwala" gyadamai kai tayi ahankali sanan tafara, shikuma ya tsaya agaban babban tap yayi nashi sharp sharp yagama yazo ta bayanta ya tsaya saida tagama sanan yasake rike hannunta suka fito, wani drawer gaban gadonta yaja yaciro dadduma ya shimfida musu sanan yahau yace "let's pray" salla yajasu raka'a biyu, daya idar yajuyo yakama goshinta batasan maiya karanta ba but ita kawai she just want to cry and cry nd cry taji dadin ranta, awanan gidan itada shi zasuyi rayuwa, jin yadagata yasa tadan kalleshi da sauri dadduman ya kwashe ya maida inda ya dauko sanan yace "let's go" hannunta yakama yajata ahankali fita sukayi daga dakin bayan ya kashe wutan, sukai sama, dakinshi yabude wani sanyin kamshi ne yadaki dakin, zaunarda ita yayi gaban kazan yace "let's eat" gyadamai kai tayi ahankali irin na wacce tacika tai fam da kukan nan duk yana lurada ita, kasama taba cokalin tayi ahankali ya yanko naman yakai bakinta yana kallonta tana kallonshi tabude bakin ahankali yasa mata sanan yaciro fork din daga bakinta, fara taunawa tayi ahankali sanan tafashe da kukan datakasa rikewa mara sauti, yakai kusan 1min yana kallonta tana kukan sanan ahankali yace "zakiyi magana da Grandma" dasauri ta gyadamai kai tana goge fuskanta, wayanshi yaciro yay dialing number Grandma yabata sanan yatashi daga wajen yana dauke kasan dan yasan baci zatayi ba yamaida kitchen yadawo da madara nai sanyi cikin cup. Ringing daya Grandma tadauki wayan, kuka sosai Du'a tasakin mata, daidai lokacin Asad yabude kofa yashigo dakin yana maida kofan yarufe yana kallonta, ahankali tace "Grandma zan dawo wajenki" dayake a speaker yasa wayan yaji Grandma tadanyi murmushi tace "common Du'a haka mukayi dake, bana zaunar dake na gayamiki aka kaiki gidan mijinki u shouldn't be crying kina cewa zaki dawo wajena, kinaso amiki dariya ne? Bama wanan ba bakisan abinda Kakarki ke nemaba kenan so kike ta tattaraki ta tafi kauyen Ikara dake" girgixama Grandma kai tayi ahankali tace "a'a" hakan yasa Grandma tace "tom from today start behaving kaman babban bace, stop this crying, ina nan Abuja Du'a banje ko'ina ba, banyi nisa dake ba, ko tari kikayi zanji, kawai Anguwace ta bambamta, kukan nan tun safe kikeyin shi sokike ciwo yakamaki?" Girgizama Grandma kai tayi kaman tana gabanta, Grandma tace "to kidena kuka Asad is there he will take care of you kinji, kitashi kije kiyi wanka ki chanza wanan lafayan kisa kayan bacci ki, kiyi baccin ki kinji, gobe da safe zan dafa miki abinci nasoya miki namomi daban daban nabama yan jere da zasuzo gobe akara gyara gidan ataho miki dashi da dambun nama da dambun kaza kinji" gyadama Grandma kai tayi tana tsayar da kukan tace "to" murmushi Grandma tayi tace "good Girl, Allah miki albarka Du'a dina, oya tashi kije kiyi wanka, saida safe" Grandma ta katse wayan, dago kanta tayi ahankali, hada ido tayi da Asad dake kallonta yana rikeda wani hadadden mug a hannunshi yace "zaki sha milk"? Girgizamai kai tayi tace "nakoshi dazu an bani" hannunshi yamika mata alamun tabashi wayanshi mikamai tayi sanan ahankali murya chan tana wasa da yatsunta tace "Ya Asad zanje nai wanka" batare daya kalleta ba yana amfani daddanna wayanshi yana sipping milk din yace "u can use this bathroom, u have clothes in that closet" yanuna mata wani kofa datazaci wani bayine ko dakine awajen, gyadamai kai tayi batare datai musu ba sanan tawuce tashiga bayin, tamaida kofan tarufe ahankali tana tsaye bamatasan mezatayi ba, takai kusan 10min atsaye ahaka, jin karan yabude kofa wanda take tunanin yaje ijiye cup ne yasa agurguje tashiga cire lafayan dake jikinta sanan tabude shower ruwa kawai ta watsa ko sabulu bata sababa taja towel din data gani fari tadaura akirji tabude kofan dasauri tana lekowa ganin babu kowa adakin yasa tawani irin fito dagudu hartana tuntube closet din daya nuna mata tasa hannu tabude tafada ciki wani irin kurma ihu tayi tasa duka hannunta akan idanunta ta runtse su gam ta tsugunna ganin Asad tsirara haihuwar uwarshi tsaye agaban babban madubi cl0set din yana combing gashin kanshi da comb. 6️⃣3️⃣ You want this book? is 500 PAY into 3107021073 aisha Muhammad first bank. chat me up directly by clicking on this link wa.me/+2347012181461 DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFI BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA MATA BA DUNIYA WA LAHIRA. Ta madubi yake kallonta yanda ta tsugunna tadaura hannayenta dasukasha lalle kan idanunta jikinta narawa tama kasa koda motsi daga tsugunnawan datayi, dan murmushin nan nashi yayi iya lebe ko ajikinshi yacigaba da combing gashin kafin ahankali yazare comb din daga kanshi ya ijiye awajen sanan yajuyo ahankali yana tafiyan nan one one batare dayama damu yadau koda bathrobe yasa ba, agabanta ya tsaya, murya chan kasa yace "Ke" zare hannayenta tayi daga kan idananun sanan tabude idanun ahankali tadago kanta bamata idasa kai fuskanshi ba maranshi datagani da cinyoyishi ga glimpse of that long thick cock yasa tai wani irin ihu tana juyamai abaya atsugunnen tace "innalillahi nashiga uku" wanan karan sosai yay murmushi dan har jerin white teeth dinshi saida suka bayyana, ahankali yadan duka yakai hannunshi kan kafadarta yadagata yana shakan kamshin datakeyi da baiso yama dainajin kamshin, juyoda ita yayi ahankali tana facing nashi, hannunshi daya yazare daga kan shoulder din nata yakama habanta yana kallon fuskanta yace "open ur eyes" ahankali tabude idanunta dahar sundan kankance tana kallonshi atsorace, ko kadan babu alamun wasa akan fuskarshi yace "kin kalli jikina ko baki kalla ba"? Wani irin dan kwalalo mayun idanunta waje tayi lips dinta na shaking tana kokarin magana amman yaki fita daga bakinta, daure fuska yayi tamau strictly yace "did u look at my body ko baki kalla ba" yanda jikinta ke rawa shi kanshi dayake rike da ita yaji, wani kallon dayamata yasa adan rude cikin innocent gently voice tace "Ya Asad wlh bansan kana cikin nan ba" tunda take maganan yake kallon lips dinta, ahankali cikin wata kalan cozy voice yana kallon kwayar idanunta yace "that means u looked at my nakedness, kin kallen tsirara kenan" wani irin yarrrr maganan yamata dayabata kunya dasauri tai yunkurin runtse idanunta hakan yasa yace "don't u dare shut ur eyes, look into my eyes and answer me, kin kalli this my well built body naked ko baki kalla ba" tuni yaga hawaye suncika idanunta hankalinta yatashi tana kallonshi bakinta narawa sosan gaske ahankali murya chan ciki tace "amman......d.....dan ka....dan ne" tai maganan hawayen na zubowa, wani mugun kallo yamata yace "did I ask u to cry for me"? Girgizamai kai tayi tanakai hannunta kan fuskan nata ta share hawayen da bayan hannunta dayabi da kallo sabida kyan da lallen ta yayi, sanan ta maida hannun kasa, ahankali yace "kin ganni naked ina combing gashi kika kuma kallen right" gyadamai kai tayi ahankali jikinta narawa tana neman fashewa da kuka amman bahali sabida yace kartamai kuka, da kyar muryanta all load up da tone na kuka tace "amman wlh Ya Asad ina gani najuya, Allah kuwan" gyadamata kai yayi yanadan yatsine fuska yace "kin tabajin karin maganan rama mugunta ga mugu ibada ne?" Girgizamai kai tayi gabanta nafaduwa tace "a'a" hannunshi daya rike habarta dashi yasaki yana kallon kwayar idanunta yace "yanda kika kalleni tsirara haka zan rama nima na kalleki tsirara kinga we are even" yay maganan yana daura hannunshi daya cire daga habarta kan inda ta chusa towel din jikinta akirji, rushewa tayi da kuka jikinta narawa sosai takai hannayenta tai folding akan kirjin nata tana kallonshi amugun rude tace "dan Allah Ya Asad kayakuri wlh bankalleka ba, Allah bazan karab......." wani mugun kallon dayamata yasa tama kasa karasa maganan, ahankali yace "nace kimin kuka ne" girgixa mai kai tayi tace "Yaa Asad kayakuri bazan karaba, plsssss" wani mugun kallo yamata sanan yakalli hannayenta datai folding akan towel din yace "ciremin those hands kona babballasu nai flushing abayi, and if u cry anan wurin saina yankaki" gyadamai kai tayi tana hadiye kukan tana kallonshi, hannunshi yadaura kan nata datai folding yace "remove them abinda kika kallan min nima nakalla" saukar da hannayenta tayi ahankali gefe yanda kirjinta ke bugawa zaka dauka zai bullo wajene, gashi ba daman kuka, ahankali yasauke kanshi yadaura kan kirjinta daya daga towel din sosai, wani irin ijiyan zuciya yasauke kafin ahankali yadauko dayan hannunshi yadaura kan cinyanta yawani taho sama dashi ahankali kaman baiso yataho, wani irin ijiyan zuciya tasauke tareda lumshe idanunta dasauri sabida yanda takeji jikinta narawa, batare daya kalleta ba har lokacin idanunshi nakan kirjinta murya chan ciki yace "open ur eyes" bude idanunta tayi ahankali tana kallon gefen fuskanshi tanajin tafiyan hannun nashi akan flat cikinta kafin gently yay landing akan boobs dinta, wani kalan ijiyan zuciya yakara saukewa, sanan gently batare daya cire hannun dagakan boobs dinba yakai kan kullin towel din data cusa cikin kirjinta yaciro. Jin kuka yazo mata wuya abinda bataso shi Ya Asad zai kara mata yasa ahankali tace "Ya Asad please I am sorryy wlh baran karab......" batama karasa maganan ba kawai ya fizge towel din duka yay wani wurgi dashi, hawaye kawai taji yazubo mata dasauri tasa hannu ta share jikinta na rawa sosai kaman anjona da chaji, hannunta tadago zata kawo takare kirjinta dashi taji ya kabar da hannun, ahankali yadaga hannunshi ya danna wani switch dakin yay bauuuuu daman wutan daya kunna was dim yanzu ya kunna full bright light, tundaga kan feet dinta dasuka sha lalle yabida kallo har zuwa kan thick cinyanta dake shining, kafin yasauke idanunshi kan gabanta dayasha lafiyayyen waxing ko silin gashi daya babu, wani irin meaty gaba gareta kalan wanda yafi dadin nan da basuda zurfi sosai, irinsu ne nan da nan ake tabo musu madadiya, he knows different and all kinds of vagina a Medicine, baisan lokacin daya lashe lips dinshi ba tareda fuzar da ijiyan zuciya yana ganin yanda jikinta kerawa kafin yabi flat cikinta da kallo gawani cibiya mai zurfi datake dashi kaman rijiya, ashawos navel da har kudi suke zuwa subiya a musu plastic surgery su sami irin cibiyan, gently yasaukar da idanunshi kan boobs dinta, ko ranan daya shasu adakinshi bai samu yamusu kallon dayake musu yauba, wani irin full, bouncy, perky and sumcious boobs ne da ita da ake kira da bamboo, tanada pointed Nipples kanana yan dugui dugui dasu, wanan karan gasping breath yayi. "Haaaaaa!" he loves nono mai nipple, duk girman boobs idan ba Nipples pointed akansu baijin zasu taba burgeshi ba, jikawai tayi yawani dauketa dasauri tabude idanunta takalleshi shima kallonta yake da idanunshi dasuka kankance, cikin muryan tsoro dabata fita da kyau tace "Ya Asad dan Allah kayaku......." bata karasa maganan ba sabida karan faduwan kwaleba da mayuka da miye miye dataji, dan hannu daya Asad yasa dawani irin mugun zafin nama duka mayukan gaban madubin closet din yazubar dasu kasa, batama karasa ganin barin dayayi ba kawai yaji yadaurata awajen yadaga hannayenta sama hands up, ya manna ajikin madubin yadanne danashi, sanan yakalleta da idanunshi dataga sun juya kawai yasa dayan hannunshi ya fizge ribbon din dake gyararren gashinta yawani irin wargazo gashin suka zubo ajikinta kafin taji yawani fizgi lips dinta, yakai free hand dinshi yadaura kan left boobs dinshi yawani chapkoshi da kyau atare dagashi har ita suka saki kara. "arrrghhhhh!" yasaki kara. 6️⃣4️⃣ Wani irin rawa da jikinta yakeyi sabida yanda yake shan bakinta dakuma yanda yake damke boobs dinta yanajan Nipples din with all his strength yasa tafara kokarin kwace hannunta daya dage sama yadanne ajikin mirror danko kadan batason agan mata boobs ballema ashamata, ko mata bataso sugani ballekuma shi namiji, yanda take kokarin fizge hannunta yasa ahankali yasaki hannayen nata batare daya sake lips dinta ba he's still kissing her dan he never gets tired of her lips, lips dinta kaman jikakken cotton tsabagen taushi, gawani serene kamshi da bakinta ke fitarwa da tun ranan daya fara kissing nata yakeso sabida yana mugun sashi yaji ya natsu, whenever he kisses her he feels complete and damn calm. Bude idanunshi dasuka kankance yayi while kissing her still yakalli fuskanta kaman jira take kukan dayazo mata tuntuni take rikeshi sabida tsoronshi ne tasakin mai sosai takai hannunta daya ahankali tadaura kan nashi dake kan boobs dinta kaman wacce zatai committing crime dan yaji yanda yatsunta ke rawa akan nashi, kafin tafizge lips dinta daga cikin nashi ahankali tadan kalleshi yanda taga idanunshi sun kankance sunyi jazur yasa jikinta ma yashiga bari tasoma kokarin hadiye kukan datakeyi amman takasa takasa ture hannunshi nashi dake boobs dinta dayake matse wa har lokacin yana kallonta dudda hannunta nakan nashi, ahankali yakai yatsanshi daidai kasan idanunta ya sharce hawayen daya zubomata, cikin wata kalan Horny voice yace "shiiiiii" gyadamai kai tayi dasauri tahadiye kukan, sosai muryanshi ta dishashe dakayr takema iya fita kaman wanda ke serious murya yace "ban gama rama kallona dakika yiba, give me ur hand" hannunta tamikamai ahankali karba hannun nata yayi yana kallon kwayar idanunta sanan ahankali yadaura akan mikakkiyar joystick dinshi, dasauri tai motsi da hannunta zata janye ya damke hannun nata akan joystick din dake dripping yana wani bankarewa sabida wani mahaukacin dadi dayaji, dan hannunta are damn soft gasu so moist kaman tai wasan ruwa, ga hannun bala'in dumi kaman wacce ke gaban murhu abun saiya hadu yasa yaji wani kalan exotic feeling a joystick din kaman zai shura, cikin muryan wanda ke cikeda sha'awa yace "Ohhh Goddd! Aaahhhhhh" yay wani kalan kara yanakai kanshi kan wuyanta yay wani irin cuddling nata yana kara damke hannun nata sosai akan buran yanaji kaman zai mutu, ahankali yakai bakinshi ya shiga kissing wuyanta, wani irin motsi tafara tana kokarin ta zulle amman ya riketa riko mai kyau, yana kissing wuyan yanayo sama kafin yasaukar da bakinshi kan kunnenta yawani zuki kunnen, ihu tayi na kuka sabida wani firrrrrrr dataji ajikinta kaman ana tafiya da feather dawisu akan fatarta tace "Ya Asad dan Allah kadena,wlh wani iri kunnen kemini, bazan kara kallon ka ba, please kadena jikina namin firrrrr" wani kalan murmushi maidan sauti yasaki yawani murza boobs din da hannunshi ke kai tana kara damke hannun da hannunta dake kai tace "washhhhh Ya Asad Asadddd" kaman badashi takeba wani irin shamata kunne yashigayi yana nishi dasauri dasauri akunnen, abinda yake mata wlh yafi kwakule kunne da abin kunne dadi, yanayi yana squeezing boobs din da kyau tun tana kama hannunshi tazoma tadena kawai hannun nata nakaine amman baya motsi tana bendin wuyanta jikin mirror yana binta yana kara hura harshen shi cikin dan karamin hole din kunnen yana screwing kunnen da kyau dayasa taji kaman zatai fitsari anan gaban madubin daya daurata akai, ganin yanda jikinta ke bari sosai tana wani kalan narkewa tana bending yana binta shima kaman tsohon maye sabida yasa yaciro harshen shi daga kunnen ahankali yana huramata iska sanan yashiga manna mata kiss tundaga kan soft kumatu har zuwa kirjinta kasan wuya, wani irin bankarewa tayi dan sosai jikinta ke wani iri, yanda ta bankare yasa boobs din suka wani turo gaba da kyau kaman suna kiranshi, wani irin kallon boobs din yake jikinshi na tsuma kaman mayunwacin dayaga abinci kissing cleavage dinta yafara yana shaking sound going towards left wanda yagama jajjan kanshi da hannunshi ahankali yake kissing din going there yana zame hannunshi kasa danshi yakeso yafara sha dan ya riga yagama murzasu yasa Nipple din yay shooting out yafito da kyau unexpectedly taji yawani irin chapke nipple dinta yawani zuka kafin yay wani uban kara da nishi kaman wani mai asma da attack dinshi yafara, yanda yakeyi kaman ba Asad ba yahau sumbatu nonon na bakinshi yamaida dayan hannunshi kan right boobs din yana matsewa yanajan Nipples din sabida yafito dashi da kyau, yana nishi yana kara bankara da ita dabatasan lokacin datai wani karkataccen kwanciya agaban madubin ba kanta yama sauka daga gaban madubin yay kasa kawai nishi take jikinta ne akan taburin, Asad baimasan kanta yay kasa ba tsabagen yanda baya hayyacin shi. "wayyo Maman mu, wayyooo nonooo, unnnnmmm I love boobs, zansha nonon nan Ammiiiiiiii" yawani jaaa maganan kaman wani dan karamin yaro da baida wayau, wani iri takeji da tunda take arayuwanta bata tabaji ba bamatasan mezatayi ba, bamata da karfi sai bankare take gawani zafi da Nipples din kemata sabida yanda Asad yake sha kaman zai tsinke mata su, ga maganganun dayakeyi kaman ba Asad ba dake kara sawa tanajin wani yirrrr kaman shocking tundaga kan yaatsun kafafunta dan batama san ya iya surutu haka ko yanama magana hakaba kaman ma baisan inda yakeba, kaman ya haukace ita zata iya rantse wa tunda tasanshi bata tabajin yamayi surutu haka ba sai in yana tareda ita barinma yau bakinshi yakasa shiru, jin yana neman tsinke mata Nipples da sha dakuma yanda yakejan dayan yasa ta daddage tawani irin dago tureshi baya tayi da duka hannunta jikinta nawani irin yammmm, kaman zai fadi haka yaji, lips dinshi sun kara pink tsabagen abubuwan dayaketa tsotsewa, dawani irin sauri ta dirko kasa daga gaban madubin tana kallonshi jikinta narawa tana komawa gefe tana kare kirjin nata da hannayenta tana kuka sosai gabaki daya a tsure take, jin ta taka abu yasa dasauri takalli kasan ganin towel dinta ne yasa ta tsugunna ahankali tana kallonshi tadauka ta dago zata daura, wani irin mahaukacin tsawa yadaka mata. "Du'a!" wlh sakin towel din tayi jikinta kawai yahau trembling ko'ina kaman balbela datai taking off a sky, "come here" yafadi ranshi abace idanunshi sunyi jajir tsabagen jaraban dake cinshi, dawani irin sauri taje gabanshi yanda jikinta ke shaking tsabagen tsoronshi yasa kawai tafada jikinshi ta kankameshi gam gam tana nishi sama sama gabaki daya tarude, baya Asad yayi zai fadi jinta ajikinshi naked ta kankameshi, hakan yasa takara kankameshi dawani irin sauri yasa hannunshi yadafa bango abinda yataimakesu kenan, bayanta yabi da kallo barinma ass dinta, jiyayi yay wani irin high kaman yasha giya, wani irin daukanta yayi yaware kafafunta zuwa side by side dinshi, sake kankameshi tayi dan dayayta kallonta gwara ta kankameshi haka baya ganin nonon ta yakalla, bude kofa yayi yafito da ita daga closet din, sanan yadaga hannunshi yakashe wutan dakin hakan yasa dakin yay dumdun ba haske ko guda yay duhu, jin yanda takara kankameshi yasa ahankali yace "are you scared"? Gyadamai kai tayi ahankali tana kara kankameshi tanajin wani kalan natsuwa aranta, zama yayi abakin gadon tareda ita tana kan jikinshi yadaurata kan cinyanshi still tana makale dashi tana nishi ahankali dake sauka akan wuyanshi dake karamai wani mahaukacin shauki da sha'awa, hannunshi yakai ahankali yadaura kan bayanta yana shafata yace "why do you keep stressing me kinamin gardama? You want punishment"? Dasauri ta girgizamai kai alamun a'a, murya chan kasa yace "good Girl" sanan ahankali yace "kinsan blow job in ur novels"? Girgizamai kai tayi alamun a'a, murya chan kasan makoshi yace "come" yay magana yana dagota daga jikinshi ya saukar da ita akasa agabanshi, murya chan kasa yace "kneel down" faduwa gabanta yasakeyi tazaci ma wani abun mugunta zai mata jakan yasa jiki asanyaye tai kneeling agabanshi ahankali yakai hannunshi yay parking gashinta gabaki daya yarike a hannunshi sanan ya kwantar da bayanshi a gadon kafafunshi shima suna kasa, sanan yakwanto da kanta, dayan hannunshi that is free yakama joystick din nashi dashi sanan ahankali yace "open ur mouth bude bakinta tayi ahankali, murya chan kasa yace "zan baki lollipop so lick it damn hard" sanan yakai kanta kan dick din yana tura dick din bakinta da dayan hannunshi cikin wani irin murya yace "sha min" ahankali takama joystick din da bakinta wani irin bankarewa Asad yayi shi kanshi baisan he is like this ba saiya jishi a hannun Du'a to shikenan zaiji tarbiyan shi yakare, ko kadan baya iya daurewa dadi saiya hau surutai. "wayyo Allah na, '''Ohhhhhhh, ouchhh, wayyo......yoooo" yawani bakare yana yana danna kanta ciki sosai. 6️⃣5️⃣ Ihun Asad da gurnanin shi yacika gidan gabaki daya, kodan sabida this is the first time mace ke shamai burane oho, amman dai yakasa natsuwa dudda Du'a bawani iyawa ta iyaba, she's just doing it base on yanda yake controlling kanta" ganin kaman zai shura lahira a hannun Du'a yasa yasa hannunshi ya jawota kaman wata yar baby yadaurata saman jikinshi yakaita chan sama ta yanda boobs dinta sukazo saitin fuskanshi baiyi wata wata ba kaman wanda kejin kishin ruwa yakama na daman yashiga sha yana gurzan dayan dayagama sha dazu, fashewa da kuka sosai Du'a tayi dudda tanajin wani yamm yamm but still zafi yan Nipples dinta suke mata, Asad baimasan tanayi ba, ahankali yazare hannunshi daya daga daga booby dayake murzawa yakai kan soft ass dinta wani irin matse ass din yayi kafin yakai mai wani lafiyayyen spank yasake matsewa yana gunji akan boobs din dayake sha, sanan gently yasa hannunshi takasanta yanabin cinyoyinta zuwa sama ahankali, tun kafin yakai head quarter yaji gabaki dayan cinyoyinta ruwa kebinsu, wani kalan slimy juice ne haka a little bit warm, wani irin rawa hannunshi yafara dawani irin sauri yajuyar da ita still boobs din na bakinshi shi yahau kanta, ganin yanda still kuka take yasa ahankali yasaki boobs din yakai fuskanshi saitin nata ya manna fuskanshi kan nata hawayen datake na shafa fuskanshi ahankali cikin wani kalan love and lallashi voice yace "stop crying Little Baby, I am all urs, I wanna make u all mine tonight, I've been patient enough ina ganinki agabana bantaba miki komiba" harshenshi yaciro gently yalashe hawayen kan fuskan tass, kafin ya manna ma idanunta kiss ahankali dayasa ta lumshe idanunta da sauri tanajin wani irin sanyi na shiganta, cikin wani irin murya yace "did you know for how long I've thought and dreamt about this night? You are the only girl the only girl Asad yataba so, and I am a maddd jealous dude inaso na tabbatar wa dakaina yau I completely own you, babu wani namijin daya isa yace zai mallaki ko ketara kayana, you belongs to me Du'a" cikin wata kalan murya yace " you belong to Mr Asad Du'a" amugun hankali yace "and I want to eat and fuck each and every part of this your sexy body, I want to f*ck this ur tiny p*ssy, I want to disvirgin you this night daganan I will make sure I f*ck u day and night, morning and evening, night and afternoon, a kitchen, abayi, alungu, agarden I will make sure I f*ck you in each and every corner na gidan nan, na gina manni yi na ajikinki ta yanda har fatanki saiya zamto kamshi na dakomi nawa yake, I will teach you how to not be able to leave without me, I will teach you how to be crazily inlove with me sai Inga ta yanda zaki rabu dani" wani irin faduwa gabanta yayi so bai manta da maganan ba, baki tabude zatai magana dasauri yace "shiiiiii quiet" hadiye maganan tayi jin yanda har tone din maganan shi ya chanza yace "you looked at me kina fadamin in rabu dake ki auri wanda kikeso, I will show u that babu namiji dat can satisfy you and take care of you kaman ni, and karki karamin maganan wani cus I can kill mutum koda kallonki naga yanayi balle yamaji yana sonki, you are mine Du'a! mine! ni kadai! ni Asad! and tonight zan tabbatar miki da hakan dat u belongs to me daga yau har gobe har eternity" yay maganan yana fizgan lips dinta da karfi yana wani irin huci yakasa manta maganganun datamai ranan barin ma na wanda ta auri wanda takeso, shi kanshi baisan ya akayi ma he's this jealous akan Du'a ba, jifa yake komutum yagani yana kallonta zai iya kashe shi, yadade yana kissing nata passionately kaman zai cinyeta wani wutar sonta na ruruwa aranshi sanan ahankali yakai hannunshi in between legs dinta, ruwan dayaji yanabin leg dinta yasa jikinshi yadauki rawa ahankali yakai hannunshi zai daura agabanta dasauri ta turemai hannu ganin zata batamai lokaci yasa yatashi bude kafafunta yayi da hannu biyun dasauri ta yunkuro zata tashi maidata yayi da hannunshi daya kawai bata ankaraba taji yadaura kanshi awajen wani irin zabura tayi zata kwace kafanta tace "Ya Asad please kayakuri karkamin irin abun ranan nan" baimaji ba yawani sa harshen shi kan cinyanta daya baci da slimy juice din yawani irin laso yirrrrrrrr taji jikinta yayi gawani shegen waiwayi da dadi dataji sabida yanda harshen shi yay sanyi kan skin dinta batasan lokacin datace "wayyooo Ya Ass....." kasa karasawa tayi jin harshen shi na wasa da labias dinta, fashewa da kuka sosai tayi dan she don't know this is dayake mata but is driving her whole body zuwa the galaxy dataji kukan ma is not enough to express feelings din datakeji kawai saita fara kaima duka akanshi tana tureshi tana ihu tana kokarin kwace kafafunta amman yariketa gamgam ta danna kanshi sosai kaman zai shiga vijah dinta ta haihoshi. Wani irin trembling uncontrollably tafara yi but still yaki barinta saima sakin kafafunta dayayi yakai hannayenshi sama ya shiga matse boobs dinta 2 in one dadi, wlh ita bazata iya cewa ga takamaiman inda kanta yakeba dan idanunta ma juyawa suke, ganin tafice hayyacinta sai firrr firrr takeji kaman mai farfadiya yasa yaciro kanshi yatashi yahau kanta yay wani irin grabbing lips dinta she don't even know tayaya hakan yafara kissing nashi back tafarayi itama ahankali danji tayi lips dinta kaman wani naman kaza ne daya dahu lugum Grandma tabata, shidewa kawai yarage Asad baiyiba jin Du'a ta kankameshi tana kissing nashi back, azuciyanshi yahau karanto addu'an saduwa da iyali kaman an tsikareta wani abu yay reversing brain dinta daidai tadawo duniya bude idanunta tayi tarr jin wani sharp pain, bata ankaraba tasakeji nabiyu, wani dan banzan ihu tasaki "wayyo Allah na Grandma zan mutu" tashiga ture Ya Asad dayawani irin kankameta kaman zai karyata yana dambe da hole din yana kokarin shiganta at all cost amman ba hanya, "Ya Asad, Ya Asad nashiga uku, wlh zan mutu wayyo Allah na, me kake min" cikin wani irin nishi da murya kaman wanda yake nakuda tsabagen dadin da yakeji saikace yashiga ne yace "I am disvirgining you Little Baby, Ohh My God, Du'a zan mutu akanki fa, haaaaaa! what is this sweet thing u have in between ur legs, baby I am obsess with u arrrghhhhh" yay kara yana kara dukan wajen koxai samu kan yashiga dudda kan bai shiga ba yanda crowns dinshi ke dukan tiny hole din yasa yana wani mad dripping dan dadin dayakeji is unexplainable, wani irin kuka Du'a tafashe dashi tanaso tai birgima tace "Ya Asad wlh wlh wlh wlh nagayamaka natuba na rantse bazan kara maka gardama ba, dan Allah kadena Ya Asad zafi, zafi nakeji" cikin wani irin murya kaman zaiyi kuka yace "I know Baby! ki daure karki zama raguwa, ahhhhh dadiiii zan mutu wanan abun dan Allah yashiga I want to feel every part of you today, Dear Lorrrdd I wanna scream I tell everyone this girl is mineeee, please let me see this hole through please God....Auuuuchhhhh" yasake dannawa, daddagewa Du'a tayi ta gantsaramai ciwo a shoulder shi dake kusada bakinta tana kuka sosai amman baimasan tanayi ba, wani irin kara Du'a tasakeyi tana neman fitowa daga jikinshi jinxai kasheta tace "nabani Grandmaaaaaa wayyooo Allah na zan mutu" daddagewa Asad yayi yachaki wajen dan kan joystick din kadan yashiga wani irin dagewa Du'a tayi tai wani irin burgima ta tureshi tafado kasa, tana kokarin tashi yafado kanta ya kankameta shi kanshi baisan meyasame shi ba kaman he's posses yawani kankameta yana bude kafafunta data harde gam yana kokarin maida abin back, cikin wani irin mugun kuka tace "dan Allah kayakuri..." ware kafafun nata yayi dasauri yasamu yasake sokawa ihun da Du'a tayi saida jijiyoyin gaban kanta duk suka bayyana tawani irin kankameshi tana masifaffen kuka, kuka taji Asad shima yasa yana turawa irin kaman mutum yana kokarin shiga ramin dayafi kiba da karfi da yaji yama rude, ya daburce, notunan kanshi sun kwance, what he's feeling is unexplainable, ganin kaman zai zauce yasa yakama bakinta datake kuka yashiga kissing dinta both hands dinshi nakan boobs dinta yawani irin runtse ido hankalinshi nakarasa gushewa yawani kara thrusting din shi kanshi yanajin yanda yake raba namominta biyu yake shiga tsakiyan naman nakamashi tsam tsam dayasa yama manta ina yake sabida azaban dadin dayakeji, yahau f*cking da sexing Du'a with so much passionate and love, jiya ke kaman yahadiyeta yakora da ruwa kawai yahuta, yama manta da virgin yake sex, Du'a tai kuka tai kuka tai kuka har hawayen ta yama kare sai nishi kawai take, kowani ango kan sarara ma Amarya amman Asad yakasa yanaso yayi but yakasa ko kadan, dayaji yashiga ma styles yafara da ita yana sumbatu kaman sabuwan kamun hauka kunsan sunfi kowa iya surutai da sambatu, he f*cked Du'a damn good da yamanta da komi 3 awesome rounds yayi da ita, wuraren 5:30 yabarta da kyar yana sucking boobs'''dinta wani wahalallen bacci yay awon gaba da dagashi har itan dan all through idanunta biyu. 6️⃣6️⃣ DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFI BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA. PAY 500 INTO 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 you can chat me up directly by clicking on this link wa.me/+2347012181461 SANARWA SANARWA SANARWA!!!!! MATAN AURE WATSAPP CLASS WILL BE BACK THIS FEBRUARY, AND REGISTRATION IS ONGOING, ZAKI SHIGA GROUP DIN WITH JUST 2K. IF YOU ARE AN OLD MEMBER ZAKI BIYA JUST 1K. THANK YOU ❤ Wuraren 6 yabude idanunshi da kyar kanshi yamai wani irin nauyi yana sarawa idanunshi sunyi luhu luhu shima dan yawahala to dis virgin a virgin no easy ooo, ahankali yazare boobs dinshi dake bakinta yakai hannunshi yakunne bedside lamp yakalli fuskarta idanunta dudda bata budesu ba amman sun bala'in kumbura sunyi jajir abinku da fara, wani irin lumshe idanunshi yayi yabude ahankali yakai yatsanshi kan soft kumatunta yashafa, murya chan kasa da bata fita sosai yace "I am so sorry Little Baby! I had to do this" sake lumshe idanu yayi sanan yabudesu yadaura su akanta she looks damn helpless a innocent acikin jikinshi har yanzu tana rikedashi hannayenta akan gefen cikinshi, shi kadai aranshi yasan yanda yakeson Du'a kaman ya kankameta and stay with her ya lallasheta in this bed yakeji, yatsanshi yadaura saman idanunta dasuka kumbura yana kallo, kafin ahankali yakai yatsan kan black long eyelash din idanunta dasuka tattare sabida tsabagen kuka ya shafasu, dan motsi kadan tayi hakan yasa ya tsareta da idanu yana kallon lips dinta dasuka kumbura sukai pink yarr sun tsotsu awurinshi, dan lashe bakinshi yayi sanan gently yakai bakinshi saitin nata ahankali yay grabbing lips din yashiga kissing dan motsi tashigayi hakan yasa yacigaba da kissing din nata ahankali yana kallon idanunta datake kokarin budesu, kafin gently tabude idanun dasukai jajir suka kankance ta kalleshi hada idanu sukayi baice mata komiba saima lumshe idanunshi dayayi yacigaba da kissing nata yana feeling wani jarababben sha'awanta fin najiya ma, ahankali hannunshi na yawo awuyanta kafin yay landing akan kirjinta yashiga murzawa, runtse idanunta tayi dan duka jikinta yay tsami ciwo yake mata jiya he tossed her like a coin takowani angle, cikin muryanta dabai fita sosai hawaye na gangaro mata daga idanu tace "Ya Asad nagaji" ahankali batare daya saki lips dinta ba yace "I know! But I am obsess with u Mrs Asad, I can't get enough of you" kissing dinta yashiga yi sosai sosai dan karma takara samin dama tai magana yana squeezing boobs gently yasa kafanshi a tsakiyan nata yana budewa, wani irin yunkurowa tayi dan kafan kadai daya taba irin azaban dataji kaman zata mutu, tashiga tsakakaninta yayi yana kama erected joystick dinshi yana kaiwa wajen shi kanshi he knows what shes going through but yakasa hana kanshi banda haka yanason yay clearing hanyan gabaki dayane tasha kukanta tagama tass yau sabida next time kartaji wani zafi, jiya bai shiga tass ba but yanzu yanaso yakarasa shigewa tass yahutashe ta wahalan hakan yasa yay addu'a ya shige wani irin kuka da Du'a take saida tabashi tausayi amman yana shiga yama dainajin kukanta yana thrusting in da karfi very well, yana surutai da kyar shima sabida yasan zasuyi bakine ya iya kyale Du'a around 8:30 nasafe, duk wanda yaga Du'a saita bashi atausayi ana cewa first night first night ita taga first night, ahankali yasaketa sanan yasauka daga gadon dasauri yarike jikin gadon shima jiri yaji yanaji. Tsugunnawa yayi ahankali gaban gadon kafafunshi akasa kaman wanda yay kneeling, hannayenshi biyu yasa ahankali yay cupping fuskanta yana kallon yanda take kuka, hannu yasa yashare mata majinan daya zubo ahankali yace "shiiiiii stop crying" yay maganan yana caressing kanta, saida tadan lafa da kukan sanan yamike yana kallon yanda suka bata carpet din dakin sanan yawuce bathroom yashiga wanka yayi da ruwa mai dumi sanan yahada mata ruwa yafito yazo yadauketa sun bata gadon a ruwan zafin yasata tsabagen wahala ihun ma takasa sai nishi kawai take, jiyayi idanunshi sunyi jajir, sosai yamata sit bath dakanshi yamata wanka sanan yafito da ita ganin sun riga sun bata wanan dakin yasa yafito da ita yasauko zuwa dakinta zaunar da ita yayi akan gadon tama kasa zama da kyau kwanciya tayi, closet dinta yashiga yadauko mata wani simple cotton gown, Sanata yayi sanan yasa towel ya tsane mata gashin dake diddiga da ruwa, yadauko hijab yasamata duk ya damu ahankali yace "zaki iya salla a kwance" gyadamai kai tayi da kyar yace "okay yi I am coming" yay kofa, juyowa yayi yasake kallonta sanan yay dan jim yawuce yafita sama yaje kafin yay komi salla yafara yi sanan yashiga closet dinshi ya kwaso wasu magunguna da allurai yafito yadawo dakinta ganinta a kwance yanda yabarta ta lumshe ido yasa ya ijiye da sauri yafita, tea yaje yahado mata mai kauri yadawo dakin, ahankali yazauna kusada ita dagota yayi yace "kinyi sallan" gyadamai kai tayi da kyar, dasauri yacire hijabin ya yar akasa, sanan ya jawota yasata ajikinshi rungumeta yayi tsam tsam, yakai kusan 1min ahaka da ita sanan yadagota ahankali yasa hannunshi ya gyara gashinta daya barbaje yakaidasu baya sanan ya manna mata peck a forehead kafin ahankali yacire yamika hannu yadauki cup din tea yashiga bata, da kyar ta iyashan rabi, sanan yamata allura bayan yabata magani tasha, komarda ita yayi ya kwantar kafin ahankali yazo tagabanta ya tsaya gown dinta yadanja sama sanan yabude kafafunta, runtse idanunta tayi da karfi, faduwa gabanshi yayi ganin yanda yaji mata ciwo sosai, ahankali yamaida kafafun nata ya ijiye. ****** Shirye shiryen zuwa sake mata jere ake da normally ake zuwa yima Amarya washe garin ranan kaita, lafiyayyen abinci Grandma tamata da kanta, tafito tasa amota ganin kowa harda Kaka banda Mami yasa takoma ciki, a dakinta taga Mami zaune tai shiru, kai tsaye tace "me kike nufi da zama anan? bazaki bisu kije ki dubo yarki na Zainab"? Kallonta Mami tayi ahankali tace "Mama nadauka uwar Amarya bata zuwa gidanta" tabe baki Grandma tayi tace "inbadai magana kike nema daga bakina ba kema dai kinsan nine mahaifiyar Du'a yanzu, so tashi ki shirya kije kidubo yarki, idan akwai abinda zaki taimaketa dashi ki taimaka mata at least for the first time today u should be there for her when she needed u the most" Mami bata karcewa komi ba, mayafinta tadauka ta tashi, Grandma tabata wani gora na jikon magani, tace "kibata wanan tasha zai taimaka mata wajen warke wa da wuri" ahankali Mami ta karba Grandma tasata agaba suka fito har gaban motan, ganinta yasa Kaka tace "wanan kuma wacce kalan fitsara ne kukeyi a Abuja uwar Amarya na zuwa gidan yarta ne" dan dariya Grandma tayi tace "muna zuwa idan takama, shiga mota kidubomin y'ata nidai" Ahankali Mami tashiga motar su Grandma da Mom sai tabe baki suke su dai yaran basuce komiba, rufe musu kofan Grandma tayi direba yajasu suka fice daga gidan......... Gabaki dayan tea datasha ta kwaromai ajiki ko kadan bai damuba, jikinta yadauki zafi sosai, gabaki daya yarude, bathroom dinta yashiga da ita yasake mata wanka yazo ya kwantar da ita, rigan jikinshi yacire yabarshi anan kasa sanan yashiga closet wani gown yakara dauko mata yasa mata, zama yayi ahankali kusada ita yakama hannunta yarike gam, ahankali yakai hannunshi zai shafa kanta yaji ana bude gate din gidan, motoci na shigowa wani kalan mugun tsaki yaja yakalleta ganin bacci yadan saceta yasa ahankali ya ijiye hannunta agefe yatashi yadauki jallabiyan shi yay sama dasauri dakinshi yashiga yanajin hayaniyan mata, dakinshi yabude yana sake sakin tsaki, wanka yashiga yafito agurguje yashiga closet, ya shirya cikin wata madddd off white jumper daya mai kyau, turare ya feffeshe jikinshi dashi sanan yadauki bakin glasses yasaka yafito ahankali yanajin muryansu afalo, key yasa yakulle dakinshi sanan yasauko ahankali daidai lokacin kanwar su Abba na shigo da Kaka sama gasu Nana, da Hawwa da Mom abayansu, tsayawa yayi tareda saukar da kanshi kasa, washe baki Kaka tayi tace "ango baka fita ba, amgwaye dake hita da sassafe, lallai ango" ahankali yace "ina kwana" dariya tayi tace "lpy lau, yanzu dai wuce katafi mata sunzo kaida dawowa gidan nan sai dare kanajina? Haka akeyi a al'adance, yaran yanzu babu abinda kuka sani iyayenku basu koyamuku komiba na al'adan mu bahaushe, ina matar taka Du'a" kanshi nakasa yace "tana dakin ta" yanuna dakin, dasauri Grandma tace "kaini dakin kinga Aisha" dasauri kanwar Abba tajata, su Nana ahankali suka gaidashi "ina yini" ciki ciki yace "fine" sanan yawuce batare daya gaida Mom ba dasauri yasauka kasa, ganin Mami zaune afalo kanta akasa yasa yaji wani kalan kunya, kanshi akasa cikeda girmamawa yace "ina kwana Mum" kasa kallonshi itama Mami tayi, ahankali tace "Asad an tashi lpy" akunyace yace "lpy lau" yawuce yana satan kallon Aneela dake tsalle afalon itadasu Amra tana binshi da kallo, da hannu ya yafitota alamun tazo dawani irin gudu tabishi hakan yasa yabude kofa yafita ya tsaya agefe yana jiran Aneela fitowa tayi tana kallonshi tace "Uncle u are very beautiful just like Du'a" dan murmushi yamata sanan yasa hannunshi a aljihu yaciro wayanshi yabata yace "give this to ur sister Du'a" gyadamai kai tayi ta karba takoma ciki shikuma yawuce yay wajen motanshi yashiga yaja yabar gidan. Aneela na shiga falon tai wajen Mami tamika mata wayan tace "Mami Uncle say I should give this phone to Ya Du'a" ahankali Mami tace "to wuce ki kaimata" kwala mata kira Mami taji Kaka tayi. "zokiga barnan da yaron nan yawa yarki Zainabu, taho nan". DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFI BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA. PAY 500 INTO 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 you can chat me up directly by clicking on this link wa.me/+2347012181461 SANARWA SANARWA SANARWA!!!!! MATAN AURE WATSAPP CLASS WILL BE BACK THIS FEBRUARY, AND REGISTRATION IS ONGOING, ZAKI SHIGA GROUP DIN WITH JUST 2K. IF YOU ARE AN OLD MEMBER ZAKI BIYA JUST 1K. THANK YOU ❤ come and join ki koyi so many amazing marriage stuff. 6️⃣7️⃣ Ahankali Mami ta tashi tana wani irin kin kunya tai sama tana hawa benen ahankali, dakin datagani abude tayi tashiga ciki ahankali, Du'a datagani kwance idanunta sunyi jajir sun kumbura yasa taji gabanta yawani irin fadi, ganin Maman ta yasa kaman jira Du'a take tamikama Ammi hannunta tana wani irin kuka kwance akan gadon, shiga cikin dakin tai dasauri ahankali Mami tazauna abakin gadon tana kama hannun Du'a dake kuka da kyar tsabagen bakar wahala ga jikinta dayay zafi sosai, dago kanta tayi ahankali takalli Su Nana da Hawwa dasauran yaran gidan yanda suka tsaya sukai charko charko suna kallonta, cire kawaici Mami tayi ahankali tace "Nana kwashe yaran nan kutafi kasa kufara aiki" kaman jira Mom take tace "koran mini yara akeyi nagadai inda ace bata raba Nanan danata mijin ba da yanzu tariga yartaki aure" cikeda masifa Kaka takalli Mom tace "kefa dadina dake kenan wani zubin sai kiyi abu kaman mai hankali wani zubin kuma kaman jaka kike wlh" cikeda bacin rai Mom takalli Kaka, dayake Kakan tafita iya bala'i tace "zoki doken karewanta kenan dan bana gane nufin kallo" takalli Su Nana tace "kukuma bazaku wuce kufita ba kunga abin yara akeyi anan ne" dasauri yaran duk suka wuce suka fita Mom tabisu abaya fuuuu bakin ciki kaman tahadiye zuciya tamutu, bataso Du'a tasami miji irin Asad ba, yama akayi tasamu, inda tasan kara zuga Kaka akori Du'a datayi saiza tasami miji haka da wlh batayiba, gashi yasameta abudurwa zaizo yama kara santa ne, Du'a batai deserving irin jin dadin nan ba da yaranta suka dace, kamata yayi Du'a tamutu da kunci, wani irin lafiyayyen kunci takeji kaman tasama gidan gobara tahuta. Ganin sun fita yasa Kaka ta tura kofan tarufe tareda saka sakata sanan tajuyo takalli Mami dake rikeda hannun Du'a dahar lokacin kuka take mara sauti tace "Zainab wani irin jarababben yaro kuka dauki yarinyar nan kuka auramawa eh? Uban wayagayamai haka akeyi? Yaran yanzu kwata kwata basusan al'ada ba, zamanin mu sai miji yafi sati biyu yana bareki dudda muna yan kauye, yau yay kadan saiya hakura, gobema yabareki kadan yahakura ahaka haryazo yabareki duka, amman wanan takadirin yaro dakuka dauki yarinya kuka bashi jibi abinda yamata saida ya bare yarinya tass saikace ance za'a rabashi da ita kokuma ana kokarin kwace mai ita, jibi yanda yarinya takoma, wlh idan haka yakeda jaraba saiya tsotse miki y'a tass yakare duk yarinya tabi tarame taki kiba haba dan Allah, dama daga ganinshi yanda yakeda uban kyan nan da tsayi haka yakeda uban jaraba iyye" itadai Mami tana zaune tana jinta takasa cewa uppan, dan masifan Kaka first class ne wlh. Kallon Aisha dake tareda ita tayi tace "je falo dan nagaji da shegen benen man dakowani gida ake zubawa tunda nazo Abuja ban hutaba kafafuna sun kusan tsinkewa, je jakata kidauko ki kawomin kaman nasan abu haka zai faru nadebo sayuwan" ahankali tace "to Umma" sanan tawuce tabude kofan tafice, Kaka tajuya tana kallon Du'a din yanda take numfashi sama sama akan gadon tace "sannu kinji, Allah miki albarka, wanan wahalan dakikaga kinyi shi zaisa mijinki ya darajaki da daraja iyayenki dan sun baki tarbiya mai kyau kuma ya shaida hakan jiya da daddare, Allah miki albarka..." tsayarda maganan tayi sabida Aisha data shigo, da ledan sayuwan karba Kaka tayi ta duba tace "yauwa itace, ungo to, jeki kicin ki wanke ki tafasa ki juyo ki kawo uwarta tasata aciki kafin anjima da yamma wajen ya warke yadaina mata zafi bacci ma zatayi" wucewa Aisha tayi tafice da sauri dan itama Du'a tabata tausayi ita dama bata tsani Du'a ba kawai ba yanda zatayi da uwar tata ce, Allah yahorema Kaka masifa yaranta ma hakuri suke daita dan ansan tsufa ne. Ko minti biyar bai dauketa ba ta tafasa tajuye ruwan tafito tazo takawo, Kaka tace "tashi Zainaba kije ki sirka, kekuma wuce kije kisamusu hannu kuyi duka aikace aikacen daya dace" wucewa tayi tafice itakuma Mami tashiga bayi dan hada ruwan, Kaka ma zaune adakin tace "ruwan yay zafi fa Zainab karya salapce" daga ciki Mami tace "to" gamawa tayi sanan tafito tazo gaban gadon, dago Du'a tayi ahankali tace "zomuje" wani irin fashewa tayi da kuka tace "wayyo Mami zan mutu" Kaka dake zaune tace "ke dalla chan raguwa tashi kitaka kafarki" da kyar Mami ta iya sauko da ita daga gadon amman Du'a takasa takawa tana wani irin kuka dayasa Mami taji tausayinta sosai, tasowa Kaka tayi tace "bari kiga natayaki" da taimakon Kaka dabawani karfin kirki ne da ita ba suka jata da kyar take ijiye kafan akasa tana mugun kuka, suna kaiwa gaban kofa saiga amai dasauri Kaka tace "yau na shiga uku, yaro zai kashemin jika eh? Ni wlh tambayata daya dan ubanshi Awdullahi Kitse ko eh ai haka Abban ku yacemin sunan shi, to dan ubanshi cemishi akayi za'a kwacemai itane? Zainab anya yaron nan basuda jinin jaraba adanginsu kuwa jibi yanda yamaida yarinya" itadai Mami batace komi ba saishafama Du'a baya datakeyi saida tagama aman sanan suka shiga da ita bayin, Kaka tafito tana kwalama Mom kira, shigowa dakin Mom tayi tanuna mata aman tace "yi sauri share aman nan ki gyara dakin nan kafin Zainaba tagama mata wanka" wani kallo Mom tama Kaka akufule, Kaka tace "bazaki yi bane nakira wata" akufule tajuya tace "bari na dauko tsintsiya tawuce tafita itakuma Kaka tasami kujera tazauna". Saida Mami taida gaske sanan tama Du'a lafiyayyen gashi dake nema ta sume mata, bayan tagama tamata wanka mai kyau sanan tafito da ita tana jikinta tanadan takawa ahankali, Kaka tai murmushi tace "kingani ba maganin nayi sosai yanzun nan jikin zai saketa, yanzu je bata kaya tasa akawo mata abinci taci zakiga sai bacci amman ma tagama yinshi da ikon Allah" wuce Mom dake shara Mami tayi suka shiga closet, shirya Du'a tayi cikin wani simple gown na atampa sabo fil tana kallon gashinta daya haukace, comb ta dauko ta taje mata gashin ahankali daya kara wani extra taushi sabida leman dake cikinshi sanan tasa ribbon tamata parking gashin nan tai dan kyan gani tai fayau kana ganinta kasan ta wahalu sanan tafito da ita Mom harta gama gyaran, Kaka tai murmushi tace "haba yanzu kika fito Amarya dake, oya kawomata abinci Zainab taci, da uban namomi" dan murmushi Mami tayi sanan tazaunar da ita ahankali da kyar ta zauna tanason ta karkace Kaka tace "ke zauna da kyau" zaman tayi da kyau tana nishi, fita Mami tayi ta debo abincin da Grandma ta dafamata da nama dayawa sanan tashigo ta ijiye agabanta kafin ta tsugunna tabude jakanta taciro maganin da Grandma tabada akawo mata, dasauri Kaka tace "me wanan"? "maganine Mama tabani nabata idan nazo" "toto bata tafara sha saita ci abincin" kaimata maganin baki Mami tayi tace "sha" ahankali tasha maganin dadi gadan yaji ya in cinta hakan yama bakinta dababu dadi sabida aman datayi dadi sosai tasha sanan ta ture, ijiye goran Mami tayi sanan tadau plate tana debo friedrice din zatakai bakinta wayan da Asad yabama Aneela takawo mata dakekan side drawer dake gefen Du'a yahau kara, kallon wayan Mami tayi batace komiba takai abincin bakin Du'a datai kaman bamatasan da wayan ba, ahankali tabude baki ta karba tana taunawa, har wayan ya katse aka kira na biyu still bata dauka ba kuma Mami batace mata kalaba akaro na uku ne da wayan ke ringing Kaka tace "waike dan gidanku ba mijinki ke kiranki ba" tai maganan tana kallon Du'a tace "dazun nan Aneela tashigo takawo miki wayan tace yace abaki, bazaki dauki wayan ba yaro duk yanachan yadamu, dauki wayan nan miskilan yarinya kawai" ahankali tasa hannunta tadauki wayan tana kallon screen din, Ammi tagani akai, ahankali tasa hannunta tadauki wayan takai kunnenta tana juyarda kanta gefe sabida Mami da Kaka batare datace komiba. Shiru yayi kusan 2min babu wanda yace wani abu, saikuma taji saukan ijiyan zuciyan shi, sanan murya chan kasa da taji damuwa aciki yace "sorrrry!" batasan mesa ba har karshen zuciyanta taji word din sorry daya gayamata, to kodan baitaba gayamata bane, yasha cin zalinta yamata mugunta kala kala but this is the first time yake apologizing, ahankali Mami ta ijiye plate din kan saman side drawer ta tashi tafita daga dakin Kaka nabinta da kallo, tabe baki tayi itama tamike tafice daga dakin tareda rufo kofa aka barta ita kadai adakin rikeda wayan akunne. Murya chan kasa calmly yace "does it still hurt" gyadamai kai tayi ashagwabe tace "uhm" shiru yadanyi, saikuma chan yadan fuzar da iska yace "indawo?" Girgizamai mai tayi da kyar tace "uhm uhm" sanan tasa hannu akan fuskanta tana share hawayen daya zubomata, ahankali yace "did u vomit again?" murya chan ciki daya shake da kuka sosai tace "uhm" fuzar da iska taji yayi, ahankali yace "me kikeso nakawo miki"? girgizamai kai tayi batare datai magana ba, ahankali yace "mezaki ci? Should I get you an Ice cream or milkshake, anything just tell me abinda kikeso I will get it for u" kasa magana tayi sai kawai tafashemai da kuka ahankali wanda koda wani zai shigo saiya natsu zaimaji karan kukan, shiru yayi yana sauraron kukan datake mai kafin ahankali yace "I am coming now" katse wayan yayi, tsabagen kukan datake tama kasa cire wayan daga kunnenta da kyar tai shiru tacire wayan daga kunnenta ahankali tana kallon wayan kafin ahankali tabude wayan, number Grandma dayay saving da Grandma taciro tai dialing, Grandma na zaune a falo tana hutawa wayanta yahau ringing, ganin number Asad yasa tadauki wayan da sauri takara akunne tace "hello" wani kalan kuka Du'a tasakin mata dawani irin sauri Grandma ta tashi tai sama dan akwai mutane a falonta, ahankali tamaida kofan dakinta ta rufe sanan tasami kujera ta zauna tana sauraron kukan da Du'a ke mata batare datai magana har lokacin ba, dan murmushi tayi cikeda hikima tace "kidena kuka everywoman must go through this phase, saisa ai nasa Mamin ki tazo dan nasan u will need her now stop crying" makema Grandma kafada tayi kaman tana gabanta cikin kuka sosai da muryanta dabaya fita sosai tace "ni wlh kizo ki daukeni Grandma gidanki zan dawo baran kara kwana anan ba wlh mutuwa zanyi, Grandma please kizo kitafi dani wlh Ya Asad mugune Grandma" baki Grandma ta rufe tana murmushi sosai ranta fess ko banza su Mom da Grandma zasuga Du'a natsassiyar yarinya ce, kuma yanzu tariga tafi karfinsu nagaba yay gaba nakasa sai tsintan hula, Allah yama Asad albarka, anatse Grandma tace "listen to me Du'a dena kukan" rage kukan tayi Grandma tace "Asad bai miki mugunta ba it's a normal thing da ma'aurata keyi, shi ake kira da auren shine auren, Asad nada iko akanki yanzu sama da ni da mahaifanki, duk randa ya nemiki a shimfida bakijeba mala'iku zasuyita tsinemiki ne, and whatever Asad did is a sign cewa mijinki na sonki Du'a and akwai lot of affection, tausayi and so tsakaninku, nariga nabama Maminki magani tabaki, ballema keda jikinki keda saurin warkewada ciwo, nan da gobe kinji sauki garau kaman ba'a yiba, and komene yafaru tsakaninki da mijinki is between u and him, kizama mai dauriyan kinji koyaya mijinki yake kizama mai dauriya kinji" gyadamata kai tayi kaman tana gabanta ()Grandma tace "good Girl, Tom stop crying kwanta kiyi bacci abinki" 6️⃣8️⃣ Katse wayan Grandma tayi ahankali ta ijiye wayan tana share kwallanta, Mami tadade agaban dakin idanunta sunyi jajir she really made a mistake arayuwanta yau yarta ne abu kedamu gata kusada ita amman takasa mata magana saidai takira kakarta awaya, hawayen daya zubomata ta share dagudu tagoge fuskanta tass sanan ahankali ta tura kofan tashiga dakin, abincin ta kalla tace "oya tashi nacigaba da baki abincin" girgixa ma Mami kai tayi tace "Mami nakoshi naci dayawa amai zanyi" zama ahankali Mami tayi kusada ita sanan ahankali ta kwanto da ita tadaurata kan cinyanta, ajiyan ahankali Du'a tasauke tai lamo da kanta ajikin Mami, Mami na shafa mata kanta tana kallon fuskanta ahaka bacci yay awon gabada ita mai nauyin gaske tana sauke ijiyan zuciya ahankali, harga Allah tanason yarta sama dakomi na duniya kawai Du'a y'ace wacce tunda ta haifeta tadinga shiga matsala kala kala tundaga kan yan uwan mijinta zuwa mutanen datasani kawayenta da sauransu ana mata kallo kaman maza takebi, bawai ta tsani yarta bane but matsaaloli da wahalan data fuskanta kan Du'a kawai yasa ta tattare yarinyar ta ijiye agefe dan kawai tasami peace na mind not knowing that was the biggest mistake na rayuwanta badadan Grandma ba da halan yanzu Du'a tamutu da depression, hawayen datake rikewa ne yaduga akan fuskan Du'a din dasauri tasa hannu tashare hawayen cikin wani kalan muryan kuka tace "I'm sorry baby, I am so sorry for all I've done to you, Du'a u are very special, you are gifted, dudda baki makaranta ba but you've archived so much in this life da wayanda ma sukeje makaranta basu samu na, and I love u so much kinji" hawayen kan fuskanta ta share ahankali tana shafa fuskanta har lokacin, wayan Asad dayay kara yasa Mami takalli wayan, dudda taga sunan bata daukaba dan tasan shine, tana kallon wayan ya katse yasake kiranta akaro nabiyu amman bata daukaba, akaro na uku ne Mami ta kwantar da ita ahankali kan gadon sanan tadauki wayan dake ringing tafito tasauko falo takwalama Aneela kira dake dinning sunacin abinci, dasauri tazo, wayan Mami tabata tace "dauka kice Ya Du'a na bacci" dasauri duk su Mom da Kaka dake falon sunacin abincin rama da aka kawo suka kalleta, daukan wayan Aneela tayi tace "Hello Ya Du'a is sleeping" saikuma tai shiru kaman magana ake mata sanan ta katse wayan takalli Mami tace "Mami Uncle say I should come with someone to come and carry something for Ya Du'a" kafin ma Mami tai magana Hawwa ta tashi dasauri tace "muje Aneela" suka wuce suka fita, Kaka ta kalli Mami tace "mijin ne yasake kira? dayake yasan yay aika aika meyace"? Ahankali Mami tace "yace yana waje wai Aneela tazo dawani Babba" tabe baki Kaka tayi tace "yaji dashi daga baya kenan bayan yabar mana aikin bannar dayayi". Dagudu Aneela ke zuwa wajen Asad dake wajen parking motocin gidan akarkashin tent yafito ya jingina da mota yay folding hannunshi akirji idanunshi sanye da glass yay wani irin bala'in kyau irin na angwayen nan Hawwa takasa daina kallonshi, karasawa sukai wajen Aneela takama hannunshi tana murmushi tace "Uncle gani" ahankali Hawwa tace "ina yini" dan gyadamata kai yayi kaman ansashi dole, jitayi guiwanta yay sanyi, yana rikeda hannun Aneela yabude bayan motan wani katoton jaka dake cike da manya manyan robobin ice cream na coldstone different flavor yaciro batare daya kalli Hawwa ba yamika mata ahankali takarba hannunta narawa dan wani irin kwarjini da cika idanu Asad kedashi, sanan yasa hannu yasake ciro wasu manya manyan paper bags guda biyu yamika mata, saikuma yaciro wani karamin jaka yabama Aneela itama tarike sanan yamaida kofan motan yarufe yadan kalli Hawwan, yatsine fuska yayi kaman ansashi dole yay magana da ita yace "it's for wife, kibata" gyadamai kai Hawwa tayi tana kallonshi kaman zata hadiyeshi yajuya yashiga mota yatada Aneela takalli Hawwa tace "Ya Hawwa muje" juyawa tayi tabi Aneela suka tafi tana kara yaba ajin Ya Asad da gayun shi, jibi yanda yake wani ciccinkunu yana daure fuska kaman bashine yay aika aika ba, lallai Du'a is just a lucky girl data sami miji irinshi inama itace. Suna shiga falo kafin kowa yay magana Kaka tace "wanan uban kayanfa" kafinma Hawwa tai magana Aneela tace "Uncle yace mukaima Ya Du'a" wani irin murmushi Kaka tayi uwar kwadayi tace "oh ni Asma'u yau naga yaro dan duniya, baimajin kunyan mu shine yasayoma matar tashi kayan dadi yakawo mata agaban mu, ai shikenan kawosu nan kiga" kai komi gabanta yaran sukayi sanan takalli Mami tace "zo ki diban ma Du'a nata dan wanan hardamu ya siyo ta ina zata cinye abubuwan nan, kawo mata plate Hawwa" dasauri Hawwa tawuce kitchen. Kaka tashiga bude sauran paper bags wani lafiyayyen yankakken gasasshen ragone mai bala'in kamshi daya cika dakin, ji Kaka tayi yawun bakinta ya katse batasan sanda tace "Allahhu Akbar bantaba sanin haka yarinyar nan keda kashin arziki ba, deba kiga Kikai mata mu cinye sauran" karban dauko plate din da Hawwa takawo tayi sanan tadebama Du'a tadauki ice-cream guda biyu su tasamata a fridge naman ma a warmer tasa takaimata dakin. Grandma kuma ta kakkasa naman tabama kowa ice cream Mom tabama nata tace "ga naki" batare da Mum takalleta ba tace "banci" Nana tabamawa tace jeki samin a fridge Du'a takara da nata idan ta tashi, naman dazata bawa Mom tajuye akan nata< batare datama nawa Mom dinba tashiga ci, su Hawwa ma ci suke abinsu sunashan ice cream wa 6️⃣9️⃣ Komawa gida yayi parking motanshi yayi sanan yafito yashiga flat dinsu, ahankali ya kwanta kan kujera kana ganinshi kaga wanda ke cikin damuwa, wayan Ammi dake aljihun gaban riganshi yaciro yana jujjuyawa a hannu yana kallo, tafiyan dayaji yasa ahankali yadago kanshi Sharif ne yasa manyan kaya yana kallonshi yana murmushi yana saukowa yace "ango kaga wani kyan daka karayi" daure fuska yayi yaharareshi yace "ina zaka all dressed up like this" "glass Sharif yasa yace " zanje wajen friends dinmu namusu godiya ne, kasan daman ninai inviting nasu all" gyadamai kai kawai yayi Sharif yafice abinshi, Gajiya yayi dazama yasake tashi he's just so restless fitowa yayi daga flat din yayi nasu, bude kofa yayi ganin babu baki yasa yaji dadi sosai ciki yashiga, Ammi yagani tafito daga kitchen rikeda wasu kuloli ganin Asad yasa tay wani kalan murmushi ijiye kulolin tayi tazo inda yake tace "Son ya kagama da wayan nawa ne" girgixa mata kai yayi yace "no, Ammi naje dakinki na kwanta" kafin ma Ammi tabashi amsa Anty Turai data fito daga kitchen din itama rikeda wasu kuloli tace "jeka kwanta Asad uban amarci dakasha jiya da daddare dayar mutane ba dole kanemi wajen bacci ba" wani irin kallon Anty Turai yayi, hararanshi tayi ta ijiye kulolin tace "dukana zakayi? Allah yaso Aneesah y'ata tahakura dakai da yanzu ita kakusan kashewa" taidan dariya sanan ahankali tace "like father like so....." Turai! Ammi takirata rai abace, tunda take bata taba maidawa Turai martani ko magana ba sai yau, ahankali tace "please ki kama girmanki" sanan tajuya ta kalli Asad tace "go to flat dinku son ganinan zuwa" gyadamata kai kawai yayi yajuya yafita, Ammi tajuyo takalli Anty Turai datai mutuwa tsaye cikeda mamaki tana kallon Ammi, ahankali Ammi tace "haba Anty Turai, kefa matsayin uba kike awajen Asad, you are his Dad sister maisa koda yaushe kyaran yaron nan kikeyi kin matsamai, so kike yamiki rashin kunya? Wani kalan magana ne haka kikemai da girmanki? Mekike nufi da like father lik....." shiru tayi jin anbude kofa dasauri tajuyo Dad ne yashigo yana sanye da malum malum fuskarshi looking so paled, Turai na ganinshi cikeda masifa tace "Yaya wlh wlh zokama matar nan maka magana ni take kallon tsabar idanuna tanama rashin kunya, yarinyar danice nan na raineta" kallon Turai yayi yace "waike maisa kincika bakar masifa ne ana biki ma bakibar masifan ba idan baki suka shigo fa haba" baki tabude zatai magana yadaga mata hannu alamun tamai shiru sanan yakalli Ammi yace "what happen?" daga shigowan Asad har zuwa abinda Turai tafadi tagayamai, ga mamakin ta gani tayi Dad yakalli Anty Turai dasauri yace "kewane yagaya miki yama yarinyar wani abu" cikeda wani irin mugun mamaki Ammi ke kallon Dad, Anty Turai tace "dazu kawayena suka kirani sukace zasuje su duba gidan Amarya shine namusu kwatancen gidan, suka kirani suna fadimini sunje ance bacci takeyi, amman sai sukaga wata mata atsakar gida na tabbatar kishiyan Maman Du'a ce dan bazatai karya ba tace ai ango yama Amarya kacha kacha ne yarinya ba lafiya" ahankali Dad da jikinshi yay wani irin sanyi yace "shi yanzu Asad bai sarara mata ba daga kaita jiya jiyan nan" wani kalan kallo Ammi tama Dad ganin yanda yabiyewa Anty Turai suna maganan banza kan rayuwan dansu Allah yasama ba yaran dukansu agidan sun fita yasa kawai tawuce tai sama, dariya sosai Anty Turai tayi tana kallon Dad tace "bana gayamaka namiji koyaya mace take inhar akwai nono da duwawu ba'a yarda dashi ba, wai Asad da da kyar ya auri yarinyar nan yana kukkumbure kumbure uwarshi na lallabashi yana cijewa shine adaren farko harya afkama yarinya kaman jira yake" kallon Anty Turai kawai Dad yakeyi yasan duk kishi da bakin cikin bai auri yarta ne ba yasa duk take haukan nan, shi batasan takanshi yakeba nashi nacinshi, wcikeda kulewa tace "shegen yaro miskilan jarababbe kawai mai bakin hali" tajuya zata sama Dad yace "Turai" ahankali tajuyo takalleshi, "zonan" yakirata babu alamun wasa, tahowa gabanshi tayi tace "gani Yaya" ba kunya yace "wai yaushe zaki tafi ne naga bamaki maganan" kallon Dad take cikeda mamaki tace "Yaya ni kake kora daga gidanka" cikin masifan da Dad kawai yaji yazomai tsabagen kishin labarin dayaji na Asad haryay sex da Du'a tace "dakika kirani cewa kikayi birthday Aneesah zakizo, daga zuwa kinzo kin tare, as it is nariga nacika ma matata aiki danma Allah yasa tanada hakuri, yaran marigayi kanina, da yarki, kema kinzo instead of kiyi shiru azauna lafiya amman ki ishi matata mai hakuri, kin takura nata, kin tasa d'ana agaba da fitina, shegen fitinanki dayasa kika bari gidan mijinki babu namijin daya iya zama dake, ki shirya yinaki yinaki ki tattara kibarmin gidana gobe inkinga dama bakin kano yan uwan su Du'a zakibi ki bisu duk kuhadu ku koma kano tare, anbar Dadda shi kadai da Nurse dinshi da Dr dayawa ki koma kicigaba da kula dashi inba hakaba zanyi mummunan saba miki, wlh duk kudin danake baki wata wata saina yanke nadeba baki, jarababbiyan fitinanniyar mata kawai" Dad yawuce fuuuu yay sama Anty Turai da kaman an kafeta awajen tabishi da kallo danyau taga masifa kai tamaga abinda yafi karfinta, mutumin datake bama labari yana responding sosai all of a sudden ya birkice mata yana surfafa mata bala'i kaman junnu sai shafeshi, abin ya masifan bata mamaki batasan kishi ke neman kashe Dad ba. Jin Anxiety na neman kasheshi gashi sai kiranta yake bata dagawa yasa yatashi kawai wuraren 5 yafice security su yabama wayar Ammi yakai mata dan bazai ma shiga gidan ba yaga matar nan sanan yashige motar shi yawuce abinshi, awani eatery ya tsaya babu abinda bai siyamata ba sanan yashiga motanshi yaja, su Mom da Kaka dukansu na falo an karasa gyara gidan fess fess, anyi mopping ansaka turaren wuta, Mami na sama tana bama Du'a data tashi tamata wanka takara gasata abinci sukaci an bude gate, dawani irin sauri Kaka ta mike tadanja labulen windown datake kusadashi gefe tace "jama'a badai mijin bane yakara dawowa ba ni Shatu kwas kwas, wanan wani kalan so yakema yarinyar nanne haka, Du'a Allah yabaki jarabatu, kai ku tashi mu tattara yinamu yinamu mutafi" tai maganan tana mikewa tsaye tana daukan mayafinta sanan takwalama Mami kira, "Zainab sakko mutafi mijin yarinyar nan yadawo" sanan takalli sauran yaran daduk suka mike tsaye harda Mom tace "kumutafi kafin shida kanshi yacire kunya yazo yakoramu" dukansu waje sukayi, Mami data gama magana da Du'a asama tacire kunya tabata shawarwari yanda zata kulada kanta sanan tamata sallama ta sanarda ita gobe zasu koma kano sanan tamata addu'a sosai, kuka kawai Du'a tafara hakanan Mami ta juya tatafi, tana saukowa kasa su Kaka nafita daga falo. Kaman jira Asad yake ganin sun fito yasa ahankali yafito daga motan, Kaka dake kallonshi tace "to mudai zamu tafi, saduwan alheri gobe war haka mun tsufa a kano, ga yarmu nan Asad amana, daga ganinka nasan yaran kirki ne karka yarda ka chanza inba hakaba nima zan chanza maka" dan murmushi yayi yana kallon Aneela da dasauri tazo takama hannunshi tace "Uncle idan mukai hutu nadinga zuwa" gyadamata kai yayi ahankali yana murmushi sanan yasa hannunshi a aljihu yaciro wrapper kudi yan 1k sababbi guda biyar zai sama Aneela a hannu dawani irin sauri Kaka tasa hannunta ta fizge tace "gani Babba zaka bama yar karaman yarinya kudi" dan karamin murmushi yayi yace "wanan na yarane, ga naki nan zan baki" wani irin washe baki Kaka tayi tace "auuuho to ungo Aneela jebama Ya Nana kowa yadauki bandir dai dai banda cuce" dasauri Aneela tawuce wajensu Nana, sanan yasa hannu yadauko dollars sababbi yan 100 100 yabama Kaka guda goma, karba tayi dagudu tana kallon kudin tana kara goge idanu, sanan yabama Aisha kanwar su Abba dasauri takarba tace "Allah amfana" sanan yabata guda goma again yace "gashi kibata" dudda bai kalli Mum ba tasan Mom yake nufi tace "Allah ampana" gama kallon kudin tass tayi sanan tamikama Asad tace "ni ka chanza min bansan kallan kudin nan ba" dariya duka yaran sukahau yi banda Mom da idanunta sukai jajir wato ita Asad yama maida banza, 50k yadauko yakara mata akai, godiya tahau mai sanan tace "kumuje mu shiga mota" wucewa duk sukayi sanan ahankali Asad yajuya yakalli Mami dake tsaye abayansu tanadan murmushi, akunyace yakarasa gabanta sanan ahankali yadan duka ya amshi handbag dinta, murya chan kasa cikeda ladabi yace "Allah ya kiyaye hanya Mom" cikeda so dakuma kunya Mami tace Ameen har gaban motan yarakata, dakanshi yasa hannu yabude mata gaban motan duk Mum na kallo, murmushi Mami tayi tashiga sanan yadauki jakanta yabata amsa tayi yamaida kofar yarufe yace "Allah ya kiyaye hanya Mom" direbansu yajasu, Kaka tace "wato harda budema Mamar matanshi kofa ni bai budemin ba, lallai wanan yaron, naga yana tura abu ajakanki meyasa miki" dasauri Mami tabude jakanta, envelope yasamata mai kyau aciki that is sealed, dasauri Kaka tace "mugani" karba tayi ta tattaba tace " wlh kudi ne, yaron nan takadiri ne, wato yafifitaki sama damu ko ai shikenan ungo kayanki" karba Mami tayi tamaida jaka batare data budeba, Sheshekan kukan da duk sukaji yasa kowa ya waigo Mom suka gani tana kuka tasa bakin gyalenta akan idanunta dasauri Nana tace "Mom menene bakida lafiyane" hannun Nana ta ture tabarke da kuka sosai dan takasa rikewa tace "wlh wlh Allah ya isa bazan taba yafewa ba, an cutar dani an cutar da y'ata, anrabata da mijinta dan gidan arziki ita kuma tag do tazo tai auren kudi anan, wlh bamu yafeba, musamman nazo bikin nanne dannaga waya kwashi yarinyar nan nai dariya nai shewa amman ni za'a gumama bakin ciki wlh Zainab dagake har yarki van yafemuku cutata dakukayi ba" kaman jira Kaka take tace " wlh tir da halinki, kin shiga uku da bakin ciki, gayamin tunda kike kintaba zuwa bikin dakika dawo gida da uban kudi, kinsan yanzu nawa muka samu akan Du'a kuwa bari namiki lissafi, ranan dasuka zo gaidamu shida suka bada miliyan biyar, ranan sa lalli suka manna miliyan kusan shadaya shida abokan shi, budan baki aka bada miliyoyi da kannenshi suka barma su Nana yaranki sabida su yan gidan arziki ne basu damu ma dakudi ba, yanzu kalli kyautan daya mana, ko kudin nan muka hada muka bawa mijinki saiya bude babban kampani, nidai Allah yawa Du'a albarka gashinan naga arziki sabida ita, babu irin zigani dabaki kan yarinyar nan ba, kika cemin mayya ce, tana zuwan miki da daddare, aljanna ce, mecece yanzu ba gashinan ba itace tai aure har mijinta ya bare ta ba, inda aljana ce ko mayya da saidai muzo muga hawan mijin takashe shi amman gashinan shine yamana wanan kyautan, bazan kara biyemiki ba, Du'a jikata ce, yar Muhammadu ce da Zainaba kiyi ki mutu shegiya mai bakin hali matsalan yaran talakawa irinki kenan yar wahala kawai" Kaka tadinga kwapkeapa mata mari Mami uppan batace musu ba sai murmushi kawai