[7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _haske writers association_💡 *5* Saida gari yayi haske sosai yayi tsit su kutti sukaji tsit suka fito daga ma6oyarsu cikeda tsoro da tashin hankalin rashin ganin mamani dasu bulama. Dakatarda sauran yayi ya ringa bin cikin hakukuwa batareda yana dogon motsiba yaje ya leqo qauyen. Tsit sai koke koken dake tashi gawarwaki kuwa gasunan kwance Jini kuwa tuni yake gudana a qauyen dabbobinsuma ba'a bariba shiyasa gawarwakin bana mutumba bana dabba ba. Saki jikinsa yayi sosai zuciyarsa tayi nauyi yasan tunda su bulama basa taredasu to kuwa sun mutu ko antafi dasu tafiyarda bar abada ba dawowa, Tafiyarda gwara mutuwa da ita sbd a qasqantaccen bawa zaka qare wasuma kafin akai wahala da azaba tareda yunwa takashesu. Komawa yayi yana daga qafa da qyar jiri na dibarsa yakirawo sauran suka shigo qauyen babu Mai nutsuwa nansuka fara tsallake gawarwaki suna birkito wainda ke kife suna duba sauran iyalan gidan dabaa ganiba. Tuni suma wasu daga cikinsu suka fara ihun kuka sbd ganin mazansu wasu kuwa sauran matansu Dan duka iyalan gidan baabah din mazansu da matansu tareda 'yayansu su talatin da takwas ne amma su ashirin da 'daya suka tsira ankashe sha hudu antafi da uku. Lokacinda suka arba da gawar baabah nan suka qara saddaqarwa nandai akayi kukan daza'ayi aka dangana Mazan dasuka saura haka aka hada gawarwakin sukaje nesa da qauyen suka rufesu suka dawo kowa yacigaba da rayuwarsa amma kullum cikin fargaba duk da sunsan mutanen bazasu dawo yanxuba sai zuwa nanda shekaru masu Dan tsawo sun kwatanci qauyen yasake cika sosai an hayayyafa yara sungirma sunxama samari da yanmata saisu sake dawowa su kwashe. Tunda dai suna tsoro haka suka sake sakewa suka cigaba da rayuwa aka nada kutti amatsayin sabon shigaba Wanda wannan karon shi akan hada mugayen makamai na itace da dafin macizai da kunamu yamaida hankali sbd yadauki alqawarin angama satarsu ana siyardasu amatsayin bayi yaqi zasu shirya daga yanxu har ranarda mutanen zasu dawo. * Abincin dake cikin jirgin nasu ne iya sukadai suci su qoshi su kama wainda suka kamo suyita duka ba ruwansu da namiji ba ruwansu da mace ga yunwa sunbarsu da ita ga qishirwa tuni wasu daga cikinsu suka fara macewa sbd muguwar tafiyace mai nisa dazata kaisu nahiyar da MENEELIK PALACE take Duk Wanda ya mutu ruwa kawai suke jefasa ahaka mutanen suka rage da damansu. Kwanansu goma sha bakwai ajirgin ruwar kafin suka isa da sassafe. Cikin mutane sittin da 'yan kai dasuka kamo mutane arba'in kawai suka iso dasu daga qauyensu bulama sauran duk sun mutu ahanya. Bayan 'yan qauyensu bulama dama sunsato wasu daga gurare da dama. Kamar kayan wanki haka aka gargadosu dukkaninsu hannuwansu a 'daure kusan da igiya 'daya sbd ajere suke. Babu Wanda zaka kalla kaga kamar baikusa mutuwaba sbd babu Wanda yake iya tsayuwa daidai sbd wahala da yunwa ga dau'da data canza musu kamanni mamani tuni kuka ya qare zuciya ta qafe banda tsanarsu asma'u ba abinda takeji sbd ganin sune sanadin zuwanta nan ga cikin jikinta haryafi na asma'u fitowa. Bulama duk wuya da azaba asma'u yakeji itada mamani sbd ganin dukkaninsu juna biyune dasu gasu mata. Kukansa da fargabarsa karsu mutu kafin a iso Basu mutuba amma dai suna kusa sbd babu mai iya jan qwaqwaran numfashi acikinsu. A inda suke baza hajar siyarda bayinsu suka xubesu nansuka rarrabu cikin mutanen dake cikeda kasuwar Dan kar agansu da yawa dakuma kalar marasa imani agane satosu sukayi ba bayi bane babbansu  tareda manyan yaransa uku suka isa gurin wani mai siyarda 'yayan itatuwa suka zauna sunacin abinci cikin farin ciki da nutsuwa. Asma'u ce ta yanke jiki ta fadi da 'dayansu ya lura yamiqe da sauri tareda yiwa ogan nuni da sauri shima ya miqe suka isa gurinta Bulama tuni yafashe da wani irin kuka sbd yasan mutuwa tayi. Ta6ata sukayi arikice 'dayan cikin wani yare mara dadin ji yace, Tanada rai yunwa da wahalace muyi saurin bata abinci karta mutu kasan dokace anan duk mai siyarwa da masarauta bayi yazo dasu suka mutu aka gano wahalace kashesa shima akeyi musamman mu da satosu mukayi idan sultan dinsu yaji yankamu za'ayi abawa zakunansa namanmu. Yawun tsoro ogan ya hadiye sbd yasan atarihin sarkin fiyedama hakan zai iyayi musu ba abin suqarasa kashetaba basuda gurin 6oye gawarta ko yarwa batareda angansuba sbd tsantsar tsaro da qa'idojin da sultan din nahiyar yake bayarwa. Da ido yayiwa yaran alama suka kwanceta tareda fakar idanun mutane suka koma can baya da ita suka siyo mata abinci da ruwa kafin suka kelaya mata ruwa ta bude ido daqyar tanajan numfashin wahala. Miqa mata abincin sukayi hannu na rawa ta kar6a daqyar take saita hannunta yashiga bakinta Nan take ta cinye abincin tanashan ruwa sai amai. Amai tayi sosai wainda yasata matuqar galabaita nantake zazzabi mai qarfi yafarasa jikinta karkarwa. Damqo gashinta ogan yayi 6acin rai da takaicin sbd ita rayuwarsu na cikin ha'dari ya bude jajayen idanuwansa sosai yace, Idan baki saki jiki kin nuna lafiyarki kalauba zan yanka mijinki agabanki na qona namansa nazuba tokarsa a takarda Nayi sigari dashi. Marinta yayi da qarfi saidata kifa cikin qasa qasa da murya yace, Kingane? Bakinta dake jini ta goge hannu na rawa ta 'daga kai idanuwanta na qara rinewa da Jan axaba. Ingiza qeyarta yayi ta fadi ta lalaba ta miqe da qyar suka koma gurin sauran bayin. Bulama na hangota gabansa yayi mummunan faduwa ya sunkuyar dakai tareda sakin sabbin hawayen baqin ciki sbd hango jini abakinta duk da tana gogewa Tafiyarma sai ha'da hanya takeyi a wahalce amma haka take daurewa sbd bin umarninsu karsu kashe bulama. Sai da rana ta fadi suna aje cikin rana baci hargwara ruwa yau anbasu ganin mutane akasuwar gashi suna tsoron akwai 'yan rahoton sultan yamma tayi sosai suntabbatarda lokacin sultan ke shaqatawa tareda 'dansa namiji qwaya 'daya tal a gurin shan iskansa dake cikin masarautarsa kuma alokacin ake bada damar kai bayi sbd kullum masarautar bata gajiya da siyan bayi sbd girma da ikonta. Isarsu masarautar yayi daidai da fitowar yarima MAHEER IBN ABDULSHAMS tareda abokinsa KHALEEFA ABDALLAH 'Dan wazirin sultan 'yan kimanin shekaru goma sha biyu biyu sun fito daga sassan hutawar sultan fadawan hudu na bayansu zasu gurin baturen malaminsu dayazo koyardasu karatu. Kallo 'daya yarima yayiwa sashen daduke ana gargadasu zuwa sashen koyarda bayi aiki ya 'dauke kai Khaleefa kuwa tsayawa yayi yana kallonsu yace, Idan nagirma zansiyawa ummyna bayinda harsu mutu suna kularmin da ita. Tsayawa yarima yayi cak tareda juyowa jin abinda khaleefa yace yasa yatuno da alqawarin dayayiwa ammynsa yauda safe cewar zai mata kyautarda mutuwace kawai zata rabata da ita sai kawai yace atsayar masa sa bayin. Cikin hanxari aka tsayar dasu batareda ya kalli gefensuba yace abashi namijin qarshe da macen qarshe ya siya amafi tsadar farashi. Jiki na rawa aka janyo bulama da asma'u dake baya aka kawosu gabansa amma daga nesa sbd warin dau'da. Still basu yake kalloba sbd iko da mulki na jinin mahaifinsa dake yawo jikinsa yace, Akaisu ke6antaccen guri a tsaftacesu abasu abinci da suturu kyautace zanyiwa mahaifina da ammynah akaro na farko. Yana fada ta wuce khaleefa yabisa yana tunanin siyawa nasa iyayen amma zaibari sai ansake kawo wasu bayin. Sukuwa dasuka kawo bayin maqudan kudaden qasar akabasu cikeda jaka suka karbe abinsu suka juya suna isa kasuwa suka siya guzurin abinci mai yawanda zai ishesu suyi wata qasar safaro wasu sudawo su sake siyarwa. Lokacinda aka ke6esu bulama aka tsaftacesu tsaf aka basu watadaccen abinci mai kyau sukaci nantake suka 'Dan murmure sukai fasali aka fito dasu aka nufi Sashen da sultan da iyalensa kowa keda part. Kallonta bulama yayi idanuwansa taf da halayen tausayin gararinda rayuwarsu da abinda zasu haifa sbd tasake shiga, Tasu qaddarar ahaka take daga 'yaya masu gata da dukiya sunkoma wasu mutane masu wani yaren dabam agarinsu baabah yanxu kuwa zasu zamo wasu bayi masu bauta kuma iyayenda zasu haihu su haifarwa iyayen gidansu wani bawan ko wata baiwar. Itama kallonsa take da ido jajir sbd sanin daganan rayuwarsu amatsayin ma'aurata ta tsaya takuma wargaje sbd ikon ganin junaba basudashi yanxu bare kebewa kosunga juna iyakarsu satar kallo ko ikon magana basudashi. Ahankali aka jasa aka shige dashi babban palon sultan cikin tsananin biyayya 'Dan Aiken yarima ya zube yace, Allah yaqarawa sultan yawan rai da lafiya tareda qarfin mulki, Ga babbar kyauta ta musamman daga yarima. Kallon bawan yayi tareda sakin wani kyakkyawan qasaitaccen murmushi kafin yakalli 'dan aiken yakalli saikin gida yace, Sarkin gida gobe tundaga 6ullowar rana aje abudewa wanda yakawo saqonnan na yarima ma'ajiyar abincin masarautar meenelik yaringa dibar duk abinda yakeso yana kaiwa gidansa harsai rana ta fadi sanann yanxu yacire rigarsa ya shimfida acika masa itada sutura mai tsananin tsada kalolo ba iyaka wanda saiya 'dauka daqyar sbd wannan ce kyautar yarima ta farko agareni Dan haka wannan itace kyauta mafi soyuwa araina kyautarda mutuwace zata rabani da ita Aje asanarda yarima kyautarsa ta faranta ran mahaifinsa ayimasa albishirda zuwa qasarda yakeson bin baturen malaminsa karatu. Jin haka Dan aike ya zube jikinsa ba inda baya rawa sbd farin ciki yadinga rero kirari da godia kafin yafice daukeda kayanda sarki yace yana nishi daqyar sbd yawansu da nauyinsu. Kallon bulama sarki yayi kafin yakalli su waziri cikin farin cikinsa dabai 6oyuba yace, Wannan kyautace daga yarima bazaiyi bautaba bawan dazai riqa kula da hutawatane daga yau anadasa. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ *1* BISMILLAHIR RAHMANIRRAHEEM For you my ummu-khulthum. Bayine da kuyangi bila adadin akowace kusurwa ta cikin babbar masarautar kowanne da aikin daya duqufa yanayi wasu nsu kuma a qaqqame suna gadin hanyoyin wucewa da kowace qofa ta cikin masarautar Dukkaninsu kalar kayansu dayane mazansu da matansu kalar dark blue Wanda zaa iya kira da uniform. Ahankali kowannansu yafara aje aikinda yakeyi yana ra6ewa gefe tareda sunkuyarda kai qasa sbd takun tahowar sarauniya Wanda sautin anklets din zinarin dake qafarta shine yake sanarda isowarta ko tahowartar tundaga nesa wanda tunda ta tashi arayuwarta ta taso agidan sarauta tasaba duk inda take sautin sarqar ke sanarda tahowarta harzuwa yanxu data manyanta sbd mulki a jininta yake. Tana qarasowa hanyar dazata shigarda ita 6angaren mai martaba sarki ta tsaya cak batareda tace qalaba tareda juyawa ahankali tadan kalli gefenta da dama. jakadiyarta dake gefenta tayi saurin matsowa tareda juyawa takalli kuyangin dake take musu baya kusan su shida kallo daya tayi musu suka ja baya ahankali suka tsaya tareda sunkuyarda kai. Boyayyar ajiyar zuciya tasauke ahankali tareda shiga qofarda aka jima da wangale mata jakadiya tabita abaya aka rufo qofar. Parlour ne mai wani irin girma da tsari dayaji adon royal chairs red and golden kamar zinari sai qyalli suke sai komai daya qawata palon yazamto shima red and golden dinne splits aircon kusan guda biyar sai aiki suke sanyi yakama palon takoina sbd wata irin dukiyace ta musamman aka narkar a palon.  Babu kowa a palon sbd palon farkone dazai sadaka da palon sarauta harzuwa turakar sarki Ta sake tsayawa cak tareda sake sakin wata sahirtacciyar ajiyar zuciya akaro na uku zuciyarta na harbawa batareda tajuyo bangaren jakadiyaba murya a karye tace, Wannan saqon na sultan(sarki) yana matuqar girgixa zuciyata sbd saqone daya zamto na baqin ciki agaresa, Duk wani bawa ko bafade yakai wannan saqon abakacin rayuwarsane shiyasa nazabi nazo na isardashi dakaina, Ajiyar zuciya mai nauyi jakadiya ta sauke tareda kallon sarauniya zaarah din cikin tausayawa acikin aranta afili tace, Allah yataimaki sultana yakuma sanyaya ranki badan kinyi rashiba yabaki ikon isarda saqon sarkin sarakuna.... Katseta sultana zaraah tayi da cewa, Haihuwa tazamar mana abar fargaba maimakon farin ciki. Uwargijiyata Allah ya sassauci fargabarki amma dakin sake kin nunawa yarima farin cikinki da qaruwar dayasamu tunda shi yanaso ahakan kuma yana godiyar Allah da arzikin qaruwa daya basa Allah ya raya abinda aka Haifa din yasa ayi alfahari da hakan gaba. Ajiyar zuciya sultana tasake tareda furta amin qasan maqoshinta kafin ta tattaro jarumta da qarfin gwiwa ta gyara zaman gyalen kanta daya rufo dogon gashinta dake kwance har bayanta Wanda shima gashin harzuwa goshinta adone na wata kyakkyawar sarkar zinari ta kai sai aka rufo gyalen doguwar rigarta dark purple dataji adon duwatsu masu shegen kyau da kyalli gyalen naja har qasa kadan. Ratsa dogon palon tayi jakadiya na bayanta ta nufi qofarda zata kaita ainihin palonsa na musamman tana zuwa wanda ke tsaron qofar ya wangale mata qofar ahankali tashiga jakadiya takoma gefe ta toge itama tana jiran fitowar uwar dakin tata. Wani palon ne na alfarma babu kowa sai qarar ac dake tashi ahankali  Zaune yake cikin shiga ta alfarma Dattijone sosai da Hutu da mulki na jinin sarauta daya ratsasa, Kallo daya yayi mata da idanuwansa masu tsananin kwarjini da firgitarwa taso rudewa tayi saurin daidaita kanta ta tattaro nutsuwa da qarfin hali. Qarasowa tayi cikin sanyin jiki da fargaba ta kallesa ta rufe idanuwanta dasuka fara canxawa murya na rawa tace, Allah yataimakeka saqo daga GEORGIA..... Idanuwan daya sake watso matane yasa taso daburcewa tayi saurin gyara murya cikin nutsuwa ta dauke idanuwanta daga kallonsa murya na rawa tace, Yarima yabugo yasanarda saqon matarsa ta sauka ansamu 'YA MACE. Sake dauke kai tayi sbd gudun ganin yanayinsa sbd kodagajin yanda ya dauke wuta tasan ran maza ya baci babu jin dadi ko alamar farin ciki dagajin saqonta. Tsawon mintuna ashirin shiru Kamar daga sama taji dakakkiyar muryarsa cikin ikon mulki yace, Kin isarda saqon yarima Dan haka kisanardashi saqonsa ya iso Ke kuma tukuicinki na sanarda saqonsa bazaki sakashi a idoba sai bayan shekara daya, Karya dawo harsai matarsa tasake samun wani cikin wannan karon anan zata haihu Zata haifi yariman da ubansa yaqi amsa. Yana gama fadar haka ya miqe zai shige turakarsa Dagowa tayi takallesa idanuwanta na canxawa zuwa kalar tausayin kanta dabazataga 'dantaba ko awannan shekarar Tsawon lokaci kenan tunda yayi aure matarsa tahaifi ya mace suka koma Georgia sarki yace karsu dawo saita sake samun wani cikin tasamu tasake haihuwar mace yasake korasu yarinyar ta rasu still yahanasu dawowa harsaita haifi namiji yanxuma gashi macen ta haifa kuma yanxunma saiwata shekara kenan kusan shekara biyar kenan rabonta da danta tana tsananin kewarsa dason ganinsa. Cikin sanyin murya tace, Allah ya huci zuciyar sarkin sarakuna Na karbi hukuncina matuqar hakan zai faranta ran sarkina Saqon yarima kuma kamar yagama isa a kunnensa ne Nabarka lafiya. Juyawa tayi ta nufi qofar tana isa aka bude mata ta fice Jakadiya tayi saurin Mara mata baya kanta asunkuye sbd ganin yanayin uwar dakin nata. Suna isa babbar qofa suka fice kuyanginta sukai saurin Mara musu baya Bayi sai zubewa suke suna sunkuyar dakai yaukam ko kallonsu bata iyayi bare amsa gaisuwarsu dankuwa ranta amatuqar dagule yake. Tana isa sashenta cikin tsananin sauri aka bude mata qofa tashiga Tana shiga kai tsaye hanyar bedroom dinta tayi bayan tasake wuce palonta na musamman inda babu mashigowa duk fadin masarautar daga ita sai danta yarima sai amintacciyar kuyangarta datake kamar matsayin 'ya agareta saikuwa jakadiya ko matar yarima bata taba shigowa nan palonba iyakacinta na farko bedroom dinta kuwa ko yarima baitaba shigaba bare jakadiya kuyangarta mai gyara mata kawai keshiga. Tana shiga bedroom din taganta a tsaye jikin wardrobe din lafiyyan dakin tana jera mata sabbin kayanta dasuka iso. Daidaita nutsuwarta da fuskarta tayi tareda gyaran murya batareda takalletaba. Juyowa tayi da sauri tana ganin sultana zaarah tasaki wani irin lafiyyan murmushin daya bayyanarda dimple dinta duka guda biyu cikin tsananin taushin murya da tsantsar ladabi tace, Ammy barka da dawowa. Daga mata kai ammyn tayi batareda sakin fuskaba kamar yanda suka sababa murya a dake tace, Ina buqatar hutu. Cikin nutsuwa tayi saurin aje kayan ta nufi qofa zata fice jiki asanyaye sbd ganin yaudai ammyn bata cikin kwanciyar hankali dankuwa tunda safe take lureda ita bata cikin kwanciyar hankali. UMMU-RUMANA....cak ta tsaya jin ammyn takirata tareda juyawa cikin ladabi tace, Allah yataimaki ammy. Bana buqatar damuwa takomai da kowa ko dogon motsi banaso kowa yafice daga nan shashen zuwa anjima saiku dawo ina buqatar Hutu. Ahuta lafiya ammy"""tace cikin sanyi tareda ficewa jiki ba dadi sbd damuwar ammy na matuqar ta6ata sbd akoyaushe idan takalleta cikin annushuwa ganin take tamkar mahaifiyartace cikin annashuwar kasancewar mahaifiyarta babbar amintacciyar baiwar ammyn kuma jakadiyarda kafin tarasu. Tana fitowa bban palon ammyn duk ta sallami sauran kuyangi da bayin sashen itama ta fita masu tsaron qofar shiga sashen kawai aka bari tareda nufar hanyarda zata sadata da bangarensu na bayi inda kowa keda daki mutum uku daki daya. #mamuhgeee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ *2* Babban sashensu na bayi da bororin masarautar ta nufa tana isa kai tsaye dakinsu ta nufa tana ganin qofar abude tasan nuratu naciki tashiga bakinta daukeda siririyar sallama. Zaune bakin katifa taga nuratun tana qoqarin zare wandon uniform dinta zata shiga wanka ta nufi bakin tata yar katifar ta zauna tana cewa, Yau kingamo da wuri Nima nasamu dan qaramin hutu daga ammy yanxu kiyi sauri kiyi wankan sai kiyimin koda kalbane sbd inason zanyi wankan tsarki banasan nayi da kaina a tsefe zai dameni tunda ba iska zaishaba koyaushe muna cikin uniform. Kallonta nuratu tayi jin yanayin data qarasa zancen dashi kamar koyaushe tun tasowarsu sun bude ido sun tsinci Kansu a bayi kuma yayan bayi Wanda har gwara ita tanada mahaifiya rumana din batada uwa batada uba. Fasa shiga wankan tayi ta qarasa katifar rumana din ta zauna tareda zame mata dankwali tace zonayi miki daga baya nayi wankan sbd nima aikine dani matuqa zanje karbo sabbin furannin dazaa jera a kwalbar ruwan dake girke palon sarauniya adama na farko gakuma aikin chanxa Gyara zama tayi cikin tausayawa rayuwarsu tace, Mamani tasha saqe saqin maganinta kuwa kafin tafita aiki? Girgiza kai nuratu tayi cikin tausayin mahaifiyarta dakuma na rumana din datake qaunar mamani da zuciya daya duk da kyararta datakeyi. Kamar rumana tasan me take tunani cikin sanyin murya tace, RUMANA INA MAI HORAR DAKE KI RIQE ALLAH AKO WANE HALI KO YANAYI KIKA TSINCI KANKI DA RAYUWARKI, IDAN KIKA RIQESA KIKA ZAMA MAI HAKURI DA DANGANA DA DAUKAR QADDARAR DAYA DORA MIKI MAI KYAWU DA MARAR KYAWU TO KODA KIKE BAIWA RAYUWA BAZATAYI MIKI TSANANIBA HAKAMA IDAN KIKA ZAMO BAIWA MAI BIN UMARNIN UWAYEN GIDANKI TO HAKAMA RAYUWA BAZATAYI MIKI TSANANIBA... Nuratu wainnan sune kalaman ummana da ako yaushe suke shawagi cikin zuciya da kunnuwana wainda sune nake kallo amatsayin wasiyyarta gareni, Ni baiwa ce uwata da ubana bayine harsuka rasu, Banida wani gata ko martabarda zan kalli kaina amatsayin wata mace ko 'ya mai qima sbd nima zanqarasa rayuwatane amatsayin baiwa kamar iyayena, Tun lokacinda nayi wayo cikakkiyar mai yanci ta hanyar 'yantawa Allah yakarbi adduata amma adaidai lokacinda yantawar batada amfani sbd tana kwance ciwon ajali Wanda yasa na yanke rai daga samun ingantacciyar rayuwa..... Katseta nuratu tayi da cewa, Ba'a cire rai daga rahamar uban giji rumana, Ki zamto mai gode masa da kowace irin niima, Ke mai saa ce sbd koda kasancewarki baiwa kinfita dabam acikin bayi sbd ke abar qaunace ga sarauniyar datafi kowace mace matsayi acikin masarautarnan sultana zaarah kasancewarki 'ya ga amintacciyar baiwarta Ko ahaka kika duba zaki godewa Allah da wannan ni'imar. Ajiyar zuciya tasauke ahankali tareda zare kanta ta juyo ta kalli nuratun tana tattare dogon gashinta tace, Kibar kitson kiyi wanka kikoma bakin aikinki da wuri sbd gudun kwana gidan kason masarauta. Tashi nuratun tayi tana jawo kayanda tafara maidawa tana cewa, Bazan samu yin wankaba kuma sbd lokaci yashiga kuma wlh tsananin aikine asashen sarauniya adama sbd komai na sashen zaa canza har sitirunta kaf ko tsokalinda aka siyo jiya bazai shiga sashentaba sai sabo dal sbd kwanaki uku zuwa hudune suka rage ta kammala hukuncinta na sultan daya bata na ko qofar palonta na farko karta fito sai bayan shekara guda iyakacinta palonta na qurya zuwa bedroom dinta ko 'yayanta anhana shiga gurinta bare kuyangi iyakacinsu palonta na farko jekadiyarta kawai keda izinin shiga sbd kamata da laifin sa likita yaje gidan 'yarta gimbiya amatullah yayi mata allurar tsarin haihuwa suda ake fatar samun 'da namiji a zuria sbd..... Rufe mata baki rumana tayi tana kallon qofa tace, Ya isa idan wani yajimu kinsan rayuwarmuce zamu qarasa a kurkuku. Saurin kallon qofa nuratu tayi ido a firgice zufa na karyo mata sbd shaf idan tafara barin baki mantawa takeda abinda zaibiyo baya sbd masarautar takasance maitsananin hukunci babu sauqi ko bata lokaci sbd tsagwaron mulki da iko ke yawo a jinin masarautar kasancewar sarkin masarautar mai tsananin zafine da zallar mulki babu sauki gurin daidaitawa kowa kansa, Kwarjininsa ikonsa kesa ko matansa da 'yanyansa ke matuwar shakkar hukuncinsa shiyasa kowa a kiyaye yakeda umarninsa bare 'yan fada da sauran hakiman sarki. Kusan atare suka fito daga dakinsu suka jawo dakin suka kowa yanufi gurin aikinsa Kai tsaye rumana sashen sultana zaarah takoma inda ta tararda dukkanin wasu kuyangin sashen a qofar sashen sun jeru zai zufa suke sbd tsayuwa gashi babu ikon zaunawa haka itama tabi layinsu suka cigaba da tsayin jiran lokacinda uwar dakinsu zata gama hutawa sukoma ciki domin hidimarta. Saida rana tafadi lis kafin ta matsa sbd lokacinda ake diba nabawa sarauniya Hutu yayi idan bata fitoba ana shiga aga lafiyarta Matsu tsaron bakin qofar sashen sukayi saurin bude mata tashiga tana goge zufanta ta tsaya a palon farko saidatayi mintuna kusan shida atsaye AC ya butsarda ita kafin ta nufi palon gaba tashiga da sallama Mara qarfi sbd gudun yin hayaniyar da ammyn bataso. Shigarta yayi daidai da fitowar sultana din daga bedroom dinta cikin doguwar riga maroon dataji adon sequence stones masu masifar kyau sai qyalli suke wannan karon babu adon sarqar zinari a gashinta da wuyanta kamar koyaushe saidai wasu awarwaron zinari masu kauri da girma sosai hakama babu kwalliya afuskarta kamar koyaushe sbd sultana zaarah takasance yar sarautar qasar Morocco koyaushe cikin tsananin ado da kwalliya take musamman gwalagwalai naban mamaki hakama bazaka gantaba kace tanada babban jarumin 'da sbd zamanta kyakkyawar mace mai kyawun jiki. Durqusawa tayi cikin tsananin ladabi tace, Barkada fitowa ammy da fatar kinhuta lafiya. Zama ammyn tayi kan 'daya daga cikin royal chairs din palon batareda takalli rumanarba ta 'daga kai kafin tace, Rumana 'yau banason dogon motsi bare hayaniya Dan haka kisanarda sauran ayi komai cikin qanqanin lokaci kowa ya fice kema ki kammala kije kihuta bana buqatar kowa. Angama ammy. Miqewa tayi taje tasanarda sauran kuyangin tadawo ta nufi bedroom din ammyn tafara gyara ta canza zanin gado sbd kwana daya 'daya yakeyi acire asaka sabo tana gama gyara koina ta sassaita AC daidai yanda ammy keso sanyinsa ya kasance takunna burners qamshi yafara tashi ta shiga toilet tayi gyaran dazatayi ta fito taje takarbo abincinta a manya manyan tururuwa ta jera a makeken royal dining din dake palon ta dawo gabanta ta durqusa a ladafce tace, Allah yasa ahuta lfy yakuma tasheki lfy. Ficewa tayi lokacin tuni aka fara kiran magriba daidai zata fito dake jakadiya dake qoqarin daidaita nutsuwarta tashigo. Tsayawa jakadiya tayi a palon farko tafitarda numfashi mai zafi sbd sotake ta daidaita kanta sbd da rayuwartace amatuqar tsaka mai wuya duk tabari fargabarta tasa sultana tagano hukuncin da sultan ya yanke akan alamarin dake damun masarautar shekara da shekaru. Tunda suka baro gurin sultan dazu tasake komawa sbd kai saqon banhakuri da tubar uwargijiyarta bisaga saqo Mara dadi data kaimasa na haihuwar mace da matar yarima tayi. Abakin qofar fadar ta wuni tsaye cikin rana Dan nuna banhakurin uwargijiyarta Wanda saida rana ta fadi lis sarki ya aikoda izinin shigowarta. Jiki na rawa ta zube gabansa cikin tsananin girmamawa tace, Allah ya huci zuciyar sarkin sarakuna, Sarkinda yafi kowane sarki adalci, Da yardar Allah sai anmaka takwara harsai andarje a jininka, Ba 'daya za'a samuba ba biyuba dozin ne da yardar ubangiji saika gansu saika aurensu Allah ya sake hutar zuciyarka. Gyara murya yayi cikin wani irin iko da umarni dake nuni magana daya yakeyi yace, Jakadiya aje aciro 'yan mata biyar dasukafi kowa kyawu acikin kuyangun masarautarnan a killacesu afara kintsasu daga yanxu harzuwa nanda shekara daya lokacinda yarima zai dawo Za'a kaisu sassansa amatsayin sa dakokinsa duk wadda ta haifi namiji ayimata albishirda tazama uwar sarkin wata rana. Amatuqar kidime jakadiya zufa ya keto mata murya na rawa tace, Angama sarki mai adalci, Cika umarninka zaifara ne daga yanxu, Allah dai yaqara hutar zuciyarka Nabarka lafiya. Fitowa tayi saida ta tabbatarda tayi nisa da sassasansa ta tsaya gefe tareda sharshe zufar daketa faman karyo mata tayi shiru tsawon mintuna zuciyarta na tumamin hukuncinda sarki ya yanke dakuma sanin waye yarima akan tsantseni matarsama da yaya akasamu yayi auren bare sa 'daka har biyar... Sake sharce zufa tayi cikin tsananin fargaba gashi abakacin ranka matuqar sarki ya yanke umarni katsaya sanarda wani batareda ka cika umarninba Dan haka batada ikon fadawa kowa saidai kawai aiwatarwa. Nufar sassan sultana tayi cikeda fargaba da tausayinta ta yanda hankalinta zai matuqar tashi duk randa taji zata fara shirin tarbon jikokinta na sa'dakoki. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *3* Asma'u bilalu bulama shine asalin sunan mahaifiyarta asalinta 'yar qasar Nigeria ce ubanta bilalu dan Maiduguri sai mamarta ummu-rumana shuwah ce. Bilalu bulama Nada tarin dukiya mai yawa hakama matarsa ummu-rumana kasancewarta tanada gadon iyayenta dasuka barmata., 'Yarsu qwaya 'daya tak aduniya Nana asma'u wadda duk wata soyayyarsu da burinsu sun 'dorasa akanta. Bilalu bulama Nada qanne biyu jabir bulama da salmanu bulama Kowannensu matarsa 'daya da 'yaya uku uku banda bilalun dakeda 'ya daya, Jabir babban dansa shine ishaq sai qannensa mata biyu hassana da husasaina, Salmanu kuwa sunan babban dansa bulama sbd sunan mahaifinsu yaci sai qaninsa babaye da yakurah. Kowannensu nada arziki daidai gwargwado amma ba kamarna bilalu ba sbd shi ba qaramin arziki Allah ya hore masa Wanda hakan yasa shedan yashiga kwadaitawa qannensa dukiyarsa nan kowannensu yafara qoqarin ganin ya cusa dansa gurin Neman 'yarsa Nana asma'u, Tun kowanne natura babban 'dansa a 6oye gurin neman soyayyar asmaun hardai kowa yafito fili yanuna buqatarsa tason nemawa 'dansa auren, Alhaji bilalu baiyi tunanin komaiba saima farin ciki dayayi saidai abun daga baya lalace sbd fada da tashin hankali daya shigo ciki sbd tuni kawuna suka rarrabe sbd alamarin ganin haka sai alhaji bilalu yace abari asma'u tazaba Wanda takeso acikin yaran dakanta sbd ya fahimci bulama shine Wanda tafiso kuma maganar gaskia yafi ishaq nutsuwa da tarbiya ga hankali amma shi bazai fadaba saidai ita asma'u tafada Wanda takeso dakanta. Tashin farko da'a tambayeta gaban kowa ba 6oyo ta za6i bulama Hakan datayi shiya qulla wata irin qiyayya da sabani tsakanin jabir da yayyunsa bilalu da salmanu. Bayan auren da wata biyar aka wayi gari gidan alhaji bilalu ya qone qurmus dagashi har matarsa ummu rumana babu Wanda yafita kuma a iya binciken da akayi aka gano wutar dai kunnata akayi da man petrol. Haka akayi zaman makoki aka watse dakyar aka samu asma'u ta dangana Wanda saida aka hada da adduoi da sauke al-qur'ani kafin tadawo daidai. Duk inda hankalin alhaji jabir da ishaq yake yasake hargitsewa sbd sai yanxu kukaga wautarsu ta kashe su alhaji bilalu sbd yanxu duk tarin maqudan dukiyarsa yarsa zata gada tokuma ai mijinta da uban mijinta suzasu juya dukiyar kenandai alhaji salmanu yayi arzikinda ba ranar qarewarsa shikenan shi yatashi abanza. Cikin watanni hudu shida ishaq sunkasa sukuni suna qulla yanda zasu qwato dukiyar su raba su salmanu da ita. Ranarda suka gama qulla suka aika 6arayi gidan alhaji salmanu tsakiyar dare, Gurin karbar takardun bulama da mahaifinsa sukai gardamar bayarwa Wanda yaja nan take aka harbe alhaji salmanu da matarsa bulama naganin haka ya buge babbansu da flower verse ya fizgo matarsa asma'u suka gudo tareda takardun dukiyar Yakurah da babaye dama suna schools hostels suke zama. Gudu suke sosai atsakiyar ko gani sosai basayi sbd duhun dare amma haka suke gudu hannunsa damqe Dana asma'u suna keta duk hanyarda suka samu sbd sunajinsu abayansu biye dasu. Basu ankaraba suka gansu har sun fara barin anguwanni suna qoqarin ketawa daji amma haka suka cigaba da gudu agalabaice cikin tsananin wahala da gajiya Can wajen gari sukaga wani kangon gida daya qone suka shige tareda boyewa. Wani irin kuka asma'u tasaki jikinta na karkarwa Bulama yayi saurin saka hannuwansa ya toshe mata baki sbd takun su ishaq da barayin daya jiyo yana kusantonsu. Dudduba koina sukayi suna haskawa Allah yasa basu gansuba Iska ishaq ya daka cikin zafi da tsananin 6acin rai yana huci yakira abbansa yafada masa Cikin takaici da baqin ciki abban yace, Kutafi tashoshin motar duk garinnan kudubasu banason kowannensu da rai takardun kawai nakeso Ku karbo saiku harbesu Hakama atura su tiger duk wata station su zauna daga nesa da anhangosu sunzo station kafin sushiga aharbesu. Aje wayar yay yakallesu yace kumuje tashoshin mota amma wasu su tsaya anan sbd nasan idanma sunanan kusa idan gari ya waye zasu fito idan sun fito Ku harbesu kawai. Barin gurin sukayi sukuma su bulama najin haka koda gari ya waye sake lafewa sukayi sukaqi fitowa saida duhu yasakeyi suka fito cikin sanda suka fice tareda qarasa kutsawa cikin dajin suka fara gudu Jini sosai qafafuwansu ke fitarwa sbd ko takalmi babu maishi acikinsu ga yunwa ga wahala da kishirwa amma hakanan suka cigaba da tafiya sbd komawarsu nada matuqar ha'dari yanxu. Basu hadu da qauye ko dayaba har asuba tayi musu atsakiyar daji gashi tuni asma'u tafara riqe ciki tana murqususu cikin tsananin azaba ta durqushe agurin awahalce tace, Bulama marata zan mutu. Da sauri ya aje takardun ya durqusa ya tallafota jikinsa shima daqyar yake hade yawu sbd bakinsa daya bushe qyam ko yawu daqyar yake samun na hadiyewa a maqoshinsa ga wata irin rana mai tsananin azaba, Ko tsuntsaye babu adajin sbd a bushe yake babu damshin ruwa ko kadan itatuwan dajinma duk abushe suke babu mai inuwa. Jinin dayaga yanabiyo qafafuwantane yasa yayi saurin kallonta murya na rawar wahala yace, Asma'u cikine dake dama bansaniba? Innalillahi-wainnalaihirrajiun. Ganin tana Neman fita hayyacinta yasa ya goyata tareda daukar takardun yacigava da tafiya daqyar shima sbd shima yafara daina gani daidai. Ahaka rana takuma faduwa wani Daren yayi musu a tsakiyar jeji wannan karon kam ya tabbatarda wata duniyar suka fado sbd kalar yanayin dajin ya sauya sosai Tun yana gani har duhu yasake yi dare Yakuma tsalawa sosai cak ya tsaya tareda yanke jiki ya fadi asma'u dake bayansa ta fado da qarfi kafin ya bude idanu daqyar Dan taimakonta sai ganin yayi kamar tana gangarawa Bude idanuwansa yayi awahalce da sauri saiyaga Ashe bakin cliff suke mai tsananin zurfi da ruwa masu tsananin yawa yana miqewa daqyar kafin yakamota idanuwansa suka rufe yasake yanke jiki yafadi tareda fadawa shima. ******** Ahankali ya bude idanuwansa dake gani dishi dishi harsuka bude daqyar suna kallon sama, Lumshe idanuwan yasakeyi yabudesu yaga tabbas rufin sama bukkar karace yake ciki, Qoqarin motsawa yakeyi Dan ya yunqura yatashi aka shigo bukkar yayi saurin dagowa. Tashin namijine kamarsa dago fari tas sanyeda kayan saqi na fulani. Qarasowa yayi da sauri tareda dafasa yana cewa, Yi ahankali kana kariya aqafa. Kallon qafar bulama yayi sai alokacin yaji azaba ya lura da 'dauri amma bai damuba cikin dasashiyar murya da fargabar amsarda za'abasa yace, Ina matata? Inane nan? Ina takardun dake daure ajikina? Kwana na nawa anan? Cikeda mamaki da rashin isashiyar hausar fahimtar me bulaman ke fada yake kallonsa kafin ya gyara masa zaman qafar mai 'dori yace, Kayi hkr sbd bansan mezan fada makaba amsa daya zan iya baka shine kwananka takwas anan sauran tambayar anjima idan mahaifina yadawo ya amsa maka. Yana fadar haka ya fice Saigashi yadawo da qwaryar magani da akushin wani irin abinci kamar tuwa kamar kunu ya zauna tareda miqawa bulama yace, Gashi kaci saikasha magani. Kallon abincin bulama yayi yaga shi kama ma abincin yayi masa da aman tuwon semo amma sbd yunwa da matsuwar jin inda matarsa take ya karba ya dauke numfashi ya shanye. Ruwan magani ya miqa masa suma ya karba ba musu ya shanye. #Mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *6* Sashen sultana zaarah aka nufa da Asma'u dake waiwayen qofar sashen da aka baro bulama tanaji ajikinta shikenan sungama rayuwarsa atare saidai jiran lokaci kuma. Lokacinda aka kaita gaban sultana aka gabatarda ita amatsayin kyauta daga yarima. 'Dagowa tayi cikin wani irin farin ciki da murmushi takalli asma'u cikin sanyin lafazi tace, Allah yayiwa yarima albarka bisaga wannan kyauta. Sake kallon asma'u tayi dake durqushe gabanta tasaki murmushin farin ciki murya a tausashe tacewa jakadiyarta., Akaita abata 'daki sashen bayi abarta tayi kwana biyu ana koyarda ita aiki kafin tadawo nan tafara aikinta. Angama sultana. Daki aka bawa asma'u kuma cikin sa'a aka basu daki daya da mamani suka zauna jigum jigum kowa babu da'din zuciya kafin aka sake zuwa aka tafi dasu bayin bayi kowannensu yayi wanka aka rarraba musu uniform dinsu sukabi layi aka basu abinci kowa da 'yar tasarsa Anan ne asma'u suka hadu da bulama saidai iyakacinsu kallon juna sbd Layin maza dabam na mata dabam hakama ga dukkanin alamar tsaro da dokokinda suka lura dasu agurin babu bawanda ya isa ko yakeda ikon yiwa baiwa magana sbd tsaro dakuma gudun 6arna irinta zina. Duk wanda aka bawa samun guri yake a babban filin ya zauna yafara cin abincinsa. Daga ita harshi ba wanda ya iyacin abincin sai kallon juna suke daga nesa ba ikon magana har aka gama aka gargadasu aka rarrabasu zuwa sassan dazasu riqa aiki kullum. Kwanansu biyu da zuwa jikinsu ya'dan murmure daga yunwa sbd issashe kuma lafiyayyan abincinda ake basu sbd Sam babu yunwa ga bayin masarautar. Asma'u da bulama iyakacinsu da ganin junansu idan suka hadu gurin cin abinci. Ganin basuda yunwa kuma babu azabtarwa a masarautar yasa hankalinsu yadan kwanta suka fara maida hankali ga ayyukansu damuwar bulama 'dayace cikin jikin asma'u da mamani. Sosai asma'u ta dangana ta rungumi rayuwar dasuka tsinci kansu ayanxu tabi uwargijiyarta sbd ganin tana sake mata ba laifi. Aiki da bauta takeyiwa sultana tuquru babu kyuya ga tsafta da tsananin ladabi. Tunda sultana zaarah ta lurada cikin jikin asma'u tayi mamaki sosai ziciyarta tashiga wasu wasi takasa hkr ta tsare asma'un ta tambayeta cikin ladabi kanta na qasa tabata labarinsu kaf saidai ta boye mata asalinsu da dalilin barowarsu gida. Cikin tsananin tausayawa sultana tace, Karki damu asma'u Allah baya bacci kuma insha Allah za'a dauki mataki akan masu kamo bayin koba yanxu ba nasan zasu dawo. Sosai sultana tasa jakadiya sassautawa asma'u ayukanta sbd yanayin cikinta daya tsufa kuma sosai sultana keyiwa asma'u kyautar fresh fruits masu yawa sbd anason mai ciki ta yawaita cinsu. Kasancewarsu kusan sa'anni yasa sosai sultana tasa asma'u tasaki jiki da ita tun tana noqewa harta 'Dan sake idan tagama ayyukanta zata zauna gaban sultana suna 'Dan ta6a fira wani zubin harda jakadiya. Cikinta na isa haihuwa cikin ikon Allah suka haihu rana 'daya da mamani dake aiki sassan sarauniya adama. Dukkaninsu 'yaya mata suka Haifa sultana dakanta tasa akai mata iso ga sarki tasanar dashi matar mafi soyuwar bawansa ta haihu tasamu mace. Shiru yayi cikin jinjina alamarin bayi kuma da haihuwa amma saiya share sbd bayason sanin komai yanxu tunda anriga anyi haihuwar yabawa bulama dama yaje yaga yarsa yayi mata huduba. Koda bulama yaga 'yarsa hawaye 6alle masa sukayi sbd tarigada tafado daga bayi irinsu shikenan ita rayuwarda Allah yaxabarmata kenan. Huduba yayi mata kafin ya 'durqusa har qasa yamiqawa sultana cikin girmamawa yace, Kece kika cancanta daki za6a mata suna. Yarima daya fito sashen sultan yaqaraso sashen sultana yana shigowa yaji zancensu kai tsaye yakalli yarinyar yakalli sultana yace, Asaka mata UMMU-RUMANA.. Kallonsa sultana zaarah tayi fuskarta daukeda murmushi tace, Mahaifiya kayiwa takwara maheer. Mayar mata da murmushin kawai yayi tareda jinjina kai ahankali ya shafo fuskar jaririyar yace, Allah ya raya ummu-rumanah. Yana gama fadar haka ya wucewarsa sultana takalli bulama tace, Allah yaraya ummu-rumanah. Amin sukace cikin farin ciki da godiya harda jakadiya. Yarinyar mamani ma shine yayi mata huduba mamani tasawa 'yarta suna NURATU. Tunda asma'u ta haihu hankalinsu yasake kwantawa itada bulama tuni suka maida hankali ga bautarsu Idan zatazo sashen sultana adaki suke barin 'yayansu itada mamani daga baya sultana tace tariqa zuwa da ummu-rumanah Sosai lokaci yaja tuni ummu-rumanah ta fara girma Daga ummanta sai sultana da jakadiya tafi sabo dasu sai nuratu dasuke wasa tare a can sashen bayi mahaifinta ta saba dashi sbd ana 'Dan basa damar zuwa ganinta itada ummanta wasu lokutan da haka rayuwa tayi nisa sosai. Sultan an wayi gari baida amintaccen bawa kamar bulama sbd takai ko fita za'ayi wata qasar da amintaccen bawansa bulama yake zuwa gashi da tsananin biyayya da taka tsantsan sbd sultan nada qarfin mulki da iko sosai da wasu irin dokoki. Ummu-rumanah nada shekara goma sha hudu cif aduniya Allah yayiwa bulama rasuwa sanadiyar ciwon ciki. Anji mutuwarsa duk da kasancewarsa bawa hakadai asma'u da rumanah suka dangana da rashinsa saidai rasuwar ta ta6a asma'u sosai, Ta rasa lafiya da nutsuwar zuciya tun tana daurewa tuni ciwo ya kwantarda ita hakan tasa rumanah karbar ragamar aikinta a sashen sultana. Kwanciyar hankali tuni ta qauracewa rumanah ganin babu uba ga uwarta na jinya sosai Sultana ma tana cikin damuwar ciwon asma'un Dana matuqar tausayin rumanah sbd jin asma'u takeyi tamkar 'yar uwarta ta jini rumanah kuwa dama amatsayin 'ya take agareta sbd tun tana shan nono tayi sabo da yarinyar. Anyi maganin har andanga anbarwa Allah ikonsa amma jikin yaqi sauqi ganin haka sultana ta 'yantata nanda nan aka shelar an 'yanta baiwa asma'u. Rumanah ga abin farin ciki amma Sam batajinsa ita kadai tasan yanda takejin zuciyarta ganin mahaifiyarta sai qarayin nisa takeyi. Cikin dare Allah yakarbi rayuwar asma'u tabar 'yarta cikin wannan duniya mai ababen tsoro. Rumanah kam zuciyarta bushewa tayi sosai tabawa kowa mamakin rashin kukanta har aka kai asma'un aka dawo. Sultana zaarah lokacinda ta aika kiran rumanah tana zuwa ta durqusa gabanta kallon rumanar tayi batasan lokacinda hawaye suka taru a idonta ba tayi sauri shigewa qurya sai alokacin rumanah tasaki wani kuka daya tokare qirjinta ta zube agurin tanayinsa jakadiya tayi saurin jawota jikinta tana lallashinta. Andauki tsayin lokaci kafin rumanah tasaba da rayuwa ba iyayenta ga 6angare guda mamani Sam bata qaunarta bare ta rage maraicin rashin uwa sbd da mamani da nuratu take kallo amatsayin jininta. Sultana zaarah kuwa sosai take nuna qaunarta rumanah wanda itama rumanah tana qaunarta sbd ita take gani tana rage kewar ummanta. Da haka rayuwa taja harsuka qara zama 'yan mata ta maida hankali sosai ga bautawa ummy kamar yanda take kiran sultana zaarah. ******** ABDULSHAMS IBN ABDALLAH MUHD shine sultan na yanxu dake mulki a meneelik wani yanki na babban birnin ethopia kamar yanda kakanni da iyaye suka bar masa, Mulkinsu wani irin tsauri da zafi dashi ga wani irin qabilanci dasukedashi sbd Sam basa bayi ko borori da 'yan qasarsu saida akawo musu na wata qasar su siya shiyasa yawanci bayin masarautar daga qasashe dabam dabam suke mafi yawansu Nigeria sbd rashin tsaro na zama Dan qasa da 'yan Nigeria sukedashi. Tun lokacin mulkin kakanni a wannan zuriar ta ABDALLAH muhd basuda yawan 'yaya maza saidai mata wanda hakan yayita kawo barazana ga barin sarauta da mulki daga zuriar. Duk wani kalar arziki na duniya Allah ya hore musu shi kobana sarautataba amma banda yaya maza daqyar cikin yardar Allah suka samu namiji 'daya cikin 'yaya mata goma sha biyu da sarkin yakedasu daga matansa uku. ABDULSHAMS shine yazamto namiji daya kuma ya gadi sarautar bayan rasuwar mahaifinsa ABDALLAH. Tun yana yaro qanqani mahaifinsa yake cusa masa qaidoji da hukunce hukunce masu zafi sbd karsuyi sake sarauta tabar gidansu matuqar ba magaji sbd arubuce yaje a aje duk ranarda suka wayi gari sarki ya mutu ba magani to masarautar da duk wanda ke cikinta zasu zamo qarqashin ikon masarautar kilaimee tamkar bayi dundaga kan matan sarki da 'yayansa har bayinsu sbd wata tsohuwar muguwar gabace atsakanin masarautun. Hakan yasa duk wanda yayi mulki basa tsayawa kan matansu da qwarqwarori suke qarawa amma duk da haka sunada qarancin maza sosai sai arzikin 'yaya mata. Yanxu lokacin mulkin sultan abdulshams yanada matuqar zafi da tsanani amma duk da haka baiyi na iyayensa da sauran sarukan dasuka gabata. Zafinsa yasa dukkanin fadin qasar da zagayen ake tsoron hukuncinsa shiyasa kowa a ankare yake ba'a take dokar sultan ko acikin matansa bare 'yaya kafinma akai ga 'yan qasa da bayi. Matansa biyu sultana zaarah 'yar sultan jalaludden sarkin Libya. 'Sai sarauniya adama 'yar tsohon wazirin mahaifinsa. 'Yayansa goma cif duka mata sai yarima tak shine namiji. Sultana zaarah keda yara hudu Amatullah,hindu dakuma maryamah duk suna aure, Amatullah da maryamah a Libya qasar mahaifiyarsu suke aure sai Hindu dake aure Kuwait,yarima shine qaraminsu. 'Yayan sarauniya adama shida dukkaninsu mata kuma duka sunyi aure sai autarta najwah. Duk qwarqwarori da sultan yake kwana dasu Allah baiba ko 'daya daga cikinsu cikiba bare tahaifi 'da namiji Hakan yake tsananin 'daga hankalinsa ga tsufa yafara kamasa yarima yafito fili yafada bayada ra'ayin mulki ko wani Abu daya danganci sarauta Kwata kwata rayuwarsa bata yanayi damai sarauta sbd tunda yagama primary aka kawosa Greece karatu harya gama yacigaba da degree dinsa a los Angeles kafin yayi masters duk akan doctoring shiyasa rayuwarsa kwata kwata ta turawa ce, Daga nan yadawo da rayuwarsa a Georgia inda Yayi settling yafara aikinsa anan. Sam bai cika zuwa gidaba sbd yanayin aikinsa dakuma rashin son rayuwar masarautarsu koina mutane,koina bayi Sam shi bayason gurunda zai kasance da mutane sosai yanason free life bayason takura shiyasa yake ganin zama acan gida is a punishment. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *4* Jingina jikinsa yayi jikin darnin ginin qasar dakin da kusan rabin ginin karane ya dafe goshinsa ahankali tareda rufe ido yana zuciyarsa na tsananta fargabar kar asanardashi ba'aga matarsaba kokuma ta rasu. Qurawa qofar shigowa ido yayi yana sake tabbatarwa da kansa tabbas wata qasar suka fado sbd yanayin shigar Wanda yafita dazu da yanayin abincinsu da maganarsa tareda yanayin muhallin. Ya jima yana tanane tunanen fargaba da rashin sukuni kafin wani dattijo sosai daya manyanta ya shigo dakin da gwararriyar sallamarsa. Saurin 'dogowa daga jinginar yayi yatashi zaune daidai duk da rashin qarfin jikin dake tattareda dashi tareda zubawa mutumin ido Dan amatse yake dason jin ina matarsa take. Kallon bulama dattijon yayi kafin yajuyo yakalli 'dansa dake bayansa cikin wani yare yayi masa magana kafin cikin hausarsu da bata fita yace, Dama yatashi baka fadaminba kutti ? Bai dadeba da tashi baabah magani natsaya bashi kafin naje kiranka saigashi kadawo. Kallon bulama baaban yayi yace, Sannu da kaji,yanzudai babu inda yakema ciwo ko? Cikin qarfin hali yace, Banajin komai yanxu qafardaice idan na motsata da 'Dan zafi, Nagode sosai baabah amma Dan Allah ina asma'u mata..... Kwnatarda hankalinka matarka nanan tareda kai saidai itama tayi jinya ta rasa cikin jikinta amma ta warke sosai. Ajiyar zuciya yasake a6oye sbd ba qaramin dauke numfashi yayiba Dan gudun jin muguwar amsa. Kutti ne yasake shigowa dakin wannan karon Asma'u na bayansa bakinta daukeda siririyar sallama. Qura mata ido yayi sanye takeda kayan saqi irin nasu da wani juyayyen 'dankwali dako kanta bai rufe dukaba tayi wani irin mummunan baqi ta rame gabaki 'daya kamanninta sun fara sauyawa Wani irin tausayinta Dana kansa ya rufeshi amma dai tunda sun tsira kuma suna cikin qoshin lafiya daidai gwargwado to alhmdllh. Cikin sanyin jiki ta durqusa qasa tace, Ina wuni baabah. Lafiya lafiya mai sunan innejo mijinki ya farka daga yanxu kar asake kuka Dan ba'a kuka agidan baabah namiki uzirine kema. Duqar dakai tayi cikin sanyi ta 'daga kai sbd akwanakin datayi agidan taga dokoki da sabbin alamuran rayuwa a gidan da mutanen garin wanda cikin qanqanin lokaci ta fahimci tsantsar jahilci da rashin wadataccen ilimin addini suke ciki Dan acikin duhu suke sosai. Fita baabah yayi kutti yabi bayansa ta 'dago kai ahankali takallesa sai kawai tasaki qaramin kuka ahankali tareda toshe bakinta. Hannu yamiqa yajawota kusadashi ya rungumeta shima daurewa kawai yayi amma yasan gararin rayuwa yasamesu. Rarrashinta yayi daqyar yana cewa, Asma'u kiyi hkr insha Allah komai zai daidaita Dana sake warwarewa zamu koma gida mu fuskanci su...... Kallonsa tayi amatuqar razane tana girgiza kai tace, Yaya Dan Allah mubar maganar komawa yanxu kwata kwata nan inda muke wani yankine dabashida suna acikin wani lungun daji mai nisa daya ruwa masu yawa ya raba tsakaninsu da Nigeria dakuma wasu qasashen, Sunada kwanciyar hankali duk da suna cikin tsananin duhun ilimi da rayuwa, Jin dadi ba komai bane idan ga kwanciyar hankali da Wanda kakeso, Bamuda uwaye ko 'daya duk ankashesu su yakurah komawarmu yanxu zamu saka rayuwarsu acikin hadarine suma, Mu gwada bawa rayuwa wani chance anan sbd kwanciyar hankali da nutsuwa, Mubari gaba idan komai ya Dade da shidewa saimuje da zuriar da Allah zaibamu anan cikin kwanciyar hankali. Shiru yayi yana kallonta sbd tagama kashe masa jiki tunowa da mutuwar iyayensu kuma tabbas komawarsu saka rayuwarsu yakurah ne ahadari. Ganin yana tambabar yarda da zancenta yasa hawayenta tsananta cikin kuka tace, Yaya kadaina tuno dukiya da rayuwarmu tabaya sbd rayuwa dakai anan yafimin komawa cikin daular dazata saka mu rasa juna. Tsananin tsoro da figicin datake cikine yasa yayi saurin rungumeta yace, Asma'u zamanki cikin kwanciyar hankali yafimin wata dukiya da daular rayuwa. Satinsa biyu da farfadowa yafara miqewa kutti ne keta faman dawainiyar kula dashi Ahankali yake koyan tafiya da sanda har waje suke fita suna zago qauyen Wanda tsaf yagama gano tabbas cikin duhun rayuwa suke sbd dajine zallah saidai akwai niima kasancewar zagaye sukeda ruwa. Asma'u tuni tasaki jiki da matan gidan zuriar baabah Dan tuni aka ware musu fili acikin gidan da nufin bulama na warkewa yaje ya sassaqo icce ya Gina musu dakinsu acikin gidan. Cikin ikon Allah ya warke sosai bai tsaya wata wataba yafara binsu kutti daji baji ba gani ya zage yazama nimiji sbd dolene yasaba da baqar wahala sbd itace rayuwar garin gashi garin koina hakine mai shegen tsawo Wanda wani gurinma idan kana tahowa baka ganin mai tahowa. Cikin sati uku ya kammala musu dakinsu ita kuma asma'u matansu suka koya mata kara taringa binsu suna yowa tare harta hada musu gadansu na kara da tabarmar saqi. Ahankali suka saje suka zama 'yangari suma baabah yabasu sunan zuriarsa kasancewarsa shine shugaba agarin nan kowa agari suka sakasu cikin zuriar gidan baabah. Duk wata wahala ta rayuwa sun iya sunsaba yanxu sbd sun tasarwa shekara biyu agarin Kwata kwata kamanninsu sun tashi daga nada sunkoma wasu kamannin daban duk wani kyau da tsari suncireshi sunkoma munana kamar sauran 'yan garin Iliminsu na addini dasukazo dashi ya haskaka qauyen sbd sosai suka qararda 'yan qauyen yanxu ba laifi ilimin addini yadan yadu Dan yanxu wasunsu na wankan janaba idan sun sadu da iyalansu. Suna cikin kwanciyar hankali sosai sbd ana qaunarsu har mantawa akeda su 'din ba asalin nan bane tuni aka zama daya, Asma'u ma tuni tashiga jerin surukan gidan baabah babu bambamci Matar kutti MAMANI ce kawai ma suke samun matsala wasu lokutan sbd kishin matan sauri. Shekaru sunja sosai manyanci yafara kamasu amma har lokacin babu haihuwa sai 6ari takeyi data samu ciki kusan 6arinta biyar gashi girma yazo musu. Lokacinda baabah yabuqaci bulama ya qara aure bai musaba sbd bin umarnin baabah din Haka aka hadasa da wata 'yar maqocinsu sbd shi baabah 'yayansa mata takwas duk sunyi aure. Tuni bulama ya duqufa aikin sassaqo itace ba dare ba rana sbd yiwa kantali 'dakinda zaisata idan anyi auren danma wata uku aka dibarwa bikin sbd yasamu yin dakin cikin nutsuwa. Cikin ikon Allah asma'u Ashe tanada shigar ciki har wata biyu amma tayi shiru sbd kar ayi tunanin fasa auren Dan ko yanxu tana tunanin bazai tsayaba. Sauran sati biyu bikin cikin na wata biyar tuni yafito kowa yafahimci cikine da ita nan murna ta kaure sbd cikinta baita6a wuce wata biyu zuwa ukuba. Duk da haka tace kar bulama yafasa auren ayi kawai ta yanda zai samu 'yaya da yawa tunda yafara manyanta ba haihuwa, Hakan datayi yaqara kawo fahimta da shaquwa tareda qaunarta ga matanen qauyen tuni aka fara shagulgulan biki irin nasu na al'adarsu. Ana saura kwana biyu 'daurin aure da tsakar dare asma'u ta fito fitsari ta nufi bayinsu na kara dake baya na kowa da kowa na gidansu Tayi tagama harta juya saitaga kamar tana hango hutattaki na tahowa cikin qauyen ta bude idanu da kyau saitaga tabbas kamar mutane ne da yawa ke shigowa qauyen. Sakin butar qasar hannunta tayi ta nufi bukkarsu da sauri tashige jikinta na rawa ta tayarda bulama, Cikin sauri da magagi yatashi Dan yadauka cikinne yasamu matsala yana kallon cikinta da sauri yace, Innaje lafiyanki kuwa?sbd shine sunan datun zuwansu ake kiranta dashi sbd sunan mahaifiyar baabah ce tuni aka manta sunan asma'u. Murya na matuqar rawa tana kallon qofa qasa qasa tace, Mutane ne da hutattaki suka shigo qauyen nan na hangosu kuma...... Ihu da hayaniyarda qauyen ya 'dauka ne ya katse maganarta suka kalli qofa afirgice tayi saurin cakumosa tana cewa, Kajiko wlh mutane suke kashewa... Zabura yayi ya miqe tareda damqo hannunta suka fito tsakar gidanda kowa yafito cikin tashin hankali da firgici. Baabah cikin tsananin firgici da tashin hankali yace, Dukkaninku kubi ta bayan gari ku gudu karku tsaya saikun kai iyakar ruwa Ku shiga Ku lafe qasan ruwa masu kamen mutane ne su sayar wata qasar amatsayin bayi. Gaban bulama da innaje ya buga da mugun qarfi ya qara damqe hannunta tareda kallon fuskarta yace, Duk tsanani asma'u kadaki rabu da hannuna. 'Daga masa kai tayi hawaye na gangarowa idonta. Dukkanin zuriar gidan sukabi ta qofar baya suka fara gudu suna waiwaye cikin tsoro da tashin hankali suna tsallake gawarwakin wainda aka kashe kwance cikin jini sai gudana yake Ihun yara da mata tareda na maza saitashi yake ga huta da aka cinnawa wasu bukkokin. Sun kusan isa bakin ruwa innaje tayi tuntu6e da wata gawa ta fadi tareda sakin wani razanannen ihu tana rawar jiki Mamani dake bayansu da cikinta itama tayi saurin ra6esu da gudu zata wuce qafar innaje dake qoqarin tashi ta kifarda ita Bulama cikin tsananin hanzari ya riqosu duka su biyun ya tayar suka wuce da gudu amma sai wani tashin hankalin sukayi arba dashi domin kuwa su kutti da sauran yan gidan sun 6ace musu. Kallon mamani yayi cikin tsananin tashin hankali yace, Inane hanyarda baabah yace wadda mu bamu saniba? Tsabar musiba da tashin hankali ya rudata takasa ganewa sai rarraba idanu take tana tsima cikin kuka. Fizgarsu yayi suka nufi wata hanya da gudu Dan tsira Qaddara ta Riga fata sai gashi tsaye turus agaban shugaban qungiyar. Saurin kallon qasa yayi gaban shirgegen mutumin idanuwansa suka sauka kan gawar baabah kwance cikin jini ga rigarsa harta faraci da wuta. Bai ankaraba yaji saukar dukan gora atsakiyar kansa ya dafe kai idanuwansa suka rufe ya yanke jiki yafadi agurin. Suna ganin yanada sauran rai suka jasa aka jefa cikin qaton jirginsu na ruwa hakama innaje da mamani. Sun samu nasarar kamo mutane zama da sittin maza da mata banda yara suka gargada jirginsu na ruwa suka tafi. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *7* Maheer mutum ne mai ra'ayin kansa wanda wani baya saka masa ra'ayi, Abokansa mafi yawansu turawa ne sai 'Dan uwansa kuma abokinsa dasuka taso tare khaleefa duk da kasancewar basa guri 'daya shi khaleefa yana turkey ne amma suna yawan kasancewa tare idan zasuzo gida kokuma idan sun tafi wata qasar Hutu, Shiru shiru ne baida doguwar hayaniya bare son dogon zance amma ahaka so silent dashi Allah yayisa mai tsananin son rayuwar hutawa da shaqatawa batareda takurawa ba sam shi mutum ne maison life shiyasa kana ganinsa zakaga wayayyyan mutum da ilimi ya kustsa sosai tareda Hutu da naira. SUHAILAT BOUKAR itace gidanta yake kusadana maheer 'yar asalin Mali karatun masters dinta takeyi anan qasar Sosai take shiri da maheer kasancewar sunfara sanin junane sanadin abokinsa bell dayake itama friend dinta. Sunfara gaisawa ahankali harsuka saba kasancewarsu wayayyu masu ilimi yasa suke jin dadin zama da juna sbd kowa yasan abinda yakeyi kuma kowannansu is living a free life. Itadai suhailat tana tsananin son maheer amma ganin babu wannan ataredashi yasa tayi amfani da iliminta ta danne tareda 6oyewa koda wasa babu wanda zaice yaga alamar sonsa atareda ita sbd sanin ita mace ce meye amfanin iliminta ta wannan fannin idan bazata iya danne soyyayyar wanda baimasan tanayiba. TAKE NOTE 'yan mata pls mu koyi boye soyayyar wanda baisanma kanayiba ki daraja kanki na zamantowarki mace. Sultana ma ba laifi sundan saba da suhailat harkiranta tanayi ta gaidata. Duk lokacinda yazo gida maganar sultan 'dayace wato yayi aure asamu 'da namiji sbd dukkanin hope dinsu yanxu akansa yake Shi alamarin na matuqar basa ciwon kai da mamaki idan ana cewa yayi aure ya haifi 'da namiji He is man of his own now baiga dalilin dazaisa ace anason dole yayi aureba duk lokacinda yaji yafara buqatar kasancewa da mace zaiyi auren amma ba haka kawaiba yanxu yayi aure. Ammynsa nason yayi auren amma ita lalla6asa takeyi bakamar sultan dake son nuna masa qarfin iko ba kuma tasan tunda sultan yace maheer 'din yayi aure to kobai tashiba sai yayi masa koyasan matar kobai santaba. Hakan yasa sultana take kaiwa maheer 'din ziyara idan aka 'danja lokaci tana rarrashinsa amma dai still babu alamar zai takura kansa yayi yanda sukeso 'din shiyasa ta hakura lalla6a sultan akan abi maheer din ahankali abarsa har zuwa lokacinda zaiji ra'ayin yin auren. Wani shu'umin murmushi sultan yasaki lokacinda tagama fadar zancen wanda yasa gaban faduwa sbd tasan itama fada kawai tayi ko za'a dace yaji shawarar tata amma tasan sultan Sam baya 'daga qafa ga wanda ke masa garaje. Washe gari tun agurin sallar asuba aka bada shelar saqon sarki na bayan sallar juma'ar satin nan za'a 'daurawa yarima aure. Koda labarin ya iso kunnen sultana ajiyar zuciya kawai tayi ahankali batareda tace komaiba Dan tasan dole haka zata faru tayi magana asata kullen shekara. Haka dai cikin dauriya sultana ta daure tagabatarwa da sultan SUHAILAT amatsayin wadda yarima yake kulawa acan inda yake. Tsaf tabasa bayanin komai akan suhailat babu bata lokaci akai aike ba laifi 'yar manyan mutane ce ita da yayanta kadai iyayensu suka haifa rayuwarsu ba takura suna yin rayuwarda duk sukeso amma sbd wadatar ilimi yasa Sam basa iskanci amma rayuwa tajin dadi da Hutu babu wadda basayi musamman arziki da Allah yahorewa iyayensu. Sanin waye maheer da mugun ra'ayi akan abinda baiyi niyaba yasa sultan cewa sultana Zaarah ta koma masarautar mahaifinta batareda bawa ko 'dayaba harsai ranarda matar maheer zata shigo masarautar sushigo tare. Rintse idanuwa tayi cikin ciwon rai da tausayin maheer sbd daga ita har maheer da kowa yasan abinda sarki ke nufi da hakan Wato tayi gidansu harsai maheer ya aminta da zaiyi aure bayan yasan hakan zai ta6a tarihi da sunan masarautar mahaifinta. Kwana biyu tayi tana hada kayanta sbd tuni akayi mata booking ticket 'din jirgi. Lokacinda labari ya iso gurinsa rintse idanuwa yayi cikin daci da radadin zuciya sbd yasan me sultan ke nufi da hakan, Duk lokacinda yakeson wani Abu daga garesa da ammynsa yake yaqarsa. Bude jajayen idanuwansa yayi yakalli wayarsa ya dauka babu bata lokaci yakira sarkin isarda saqo yana 'dauka da wata irin murya mai nuna 6acin rai dayake ciki kai tsaye yace, A isarwa da sultan saqon abar ammynah ta tarbi matata ranar dayakeso. Angama sarkin saqo yafada cikin matuqar girmamawa kafin ya garzaya da hanxarinsa ya isarda saqon. Murmushin manya sultan yayi yace, Kasanar masa ranar juma'a ne saiya shirya dawowa idan kuma baidawoba ranar asabar sultana zata kawo masa matarsa har inda yake. Koda aka sake Isar masa da wannan saqon datse wayar yayi tareda rintse ido ya budesu jajir sbd baqin cikin yanda idan sultan nason quntata masa yakeyi ta hanyar ammynsa Banda son a xafafa zuciyarsa ace idan baijeba mahaifiyarsa za'asa takawo masa mata har wata qasa sbd anraina masa ita.... Wurgi yayi da tumbler din hannunsa a qule yace, Wat did he think of himself sultan dayake masa haka bayan yasan he can't tolerate seeing his ammy being disrespected. Baigama shan haushi da mamakiba saida yakoma yatararda lbarin suhailat ce amaryarsa Duk inda ransa yake saida ya sake 6aci sbd rashin tunanin dama tun farko ita 'din yagabar tun kafin aci zarafin ammynsa sbd yasan idan ya auri suhailat kowa zaiyi rayuwarda yakesone babu takura sbd dukkaninsu sunada ilimi da wayewar bawa junansu freedom batareda damuwar komaiba. Hakan yasa ba laifi ya tsaya akayi duk wani biki daza'ayi aka daura aure aka kawo amarya. Abu 'daya daya sani shine haihuwar da'akeson yayi rututu kamar ta awaki bazai yitaba sbd atsarinsa 'yaya uku zuwa hudu sun ishesa sbd gidansa da familynsa suxamto yanda yakeso baya sha'awar yara da yawa bare ayi zancen mata biyu Wanda shi yana ganin Sam bazai iya ya kwana da wancan yazo yakwana da wannan ba koba komai baya tunanin zaiso mata biyu dole 'daya zaiso so babu mgnar adalci agurin Dan haka Sam babu tsari bare mafarkin auren mata biyu arayuwarsa koba komai shi mutumne mai tsananin qyanqyami haka Allah yayisa. A ranarda aka kawo suhailat aranar yayiwa sultan yanda yakeso yayi kwanan aureda ita Satinsu biyu suka tattara suka koma Georgia shida suhailat. Suhailat tasan Sam babu so atsakaninta dashi saidai wayewarta da iliminta tareda zamantowarta free yasa yakejin dadin zama da ita kuma shima sbd yanada wadataccen ilimi da wayewa yasa Sam babu ma alamar datake nuna baya sonta as far as suna respecting juna dakuma respecting ra'ayoyin junansu ya ishesu zaman aure sabanin wasu mazan dake nuna qiyayyar mace qarara Wanda hakan ba halin namiji mai ilimi bane so pls marubuta mu gyara Sam duk namijin dayakeda ilimi da wayewa baikamata ariqa sashi yana nunawa mace tsana afiliba da kyararta,idan yanada ilimi to yayi amfani dashi. Wata uku da komawarsu ciki ya 6ullo nan saqo ya isa masarauta farin ciki da murna suka kama koina sai sadakar maqudan kudade akeyi da kyaututtuka baga masarautar ba kawai duk 'yan mineelik duk wani mai arziki kyauta da sadaka yakeyi na farin cikin insha Allah za'a samu magaji amasarautar dazata hanasu zamantowa qarqashin wata azzalumar masarautar. Lokacinda cikin ya isa haihuwa suka dawo gida ranar haihuwa kaf koina ba wani hayaniya ko 'yan kasuwanni basu firfitoba hakadai ake zaune zaman jira baga sultanba baga 'yan fadaba baga 'yan gariba, Masarautun dasuke abokantaka datasu masarautarma yau duk cikin jiran haihuwar suke suna adduar samun namiji. Bayi kuwa sunsan yau qaddara tasasu yin laifi saidai wani kan badai nakaba shiyasa kowa ya nutsu anata addua. Sultan dai yau yasan 'yancin masarautarsa ya dangana ne da abinda za'a haifa shiyasa yau tsit yake yana lazimi cikin ransa. Sultana zaarah nacan sashen da ake kar6ar haihuwar sbd haihuwar tazo da gardama Su jakadiya sai shar6e zufa akeyi ga kuyangi da bayi ajere kofar sassan haihuwar sai gumin wahala da fargaba sukeyi sbd sunsan yau duk aka haifi mace 'daya daga cikinsu ne zaije isarda mummunan saqonda qila abakin lafiyarsa ko ransa shiyasa gabaki 'daya a tsure suke da fargaba tareda adduar samun namiji. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *8* Yini guda cur masarautar tayi cikin zaman jiran haihuwar suhailat, Maheer kuwa duk yanda kowa ya 'daga hankalinsa bai 'daga nasaba sbd yasan dukkaninsu damuwarsu ba akan lafiyar matarsa yakeba sai akan abinda za'a haifane yazamo namiji, Shi tausayinsa akan suhailat din ne duk da yasan tanada dauriya sbd zama da ita yanxu yasa yasake sanin halayyarta tanada juriyar danne abu ta 6oyesa acikin ranta duk qwaqwarka yanada wuya ka gano abunda ke ranta shiyasa take matuqar basa tausayi sbd shikuma mutum ne da idan bayason Abu baya iya tsayawa basa kulawarda yakamata, Tasani babu sonta aransa amma baya nuna mata wasu halayansa ke nuna mata saidai son rayuwarsa yasa dukkaninsu jin dadin rayuwar aurensu sbd sunayintane very romantic sbd maheer romantic life is one of the best abinda yafiso arayuwarsa. Zaune yake a lafiyyan palonsa dake sashensa idanuwansa a lumshe kwata kwata bayan hot coffee dayasha dasafe har lokacin baici komaiba duk da ankawo abinci daga kicin din sashen ammynsa anjere masa dama kaidarsane bayacin abincin kowane kicin saina sashen mahaifiyarsa. Lokacinda limamin masarautar yakammala kiran sallar magriba daidai lokacin suhailat tayi wani yunquri tareda wahalallen nishi cikin tsananin azaba baby yafado. Su sultana da sarauniya adama tareda sauran 'yaya mata na zuriar gidan dake kusa duk sunzo suka miqe kusan atare kowa na kallon quryar 'dakinda suhailat din take ciki. Bayi da kuyangi tuni suka sake gyara tsayuwa suna hadiye yawun fargabar meza a fito ace anhaifa. 'Daga jaririyar mai karbar haihuwar tayi tareda kallonta taga mace ce aka haifa Ta 'dago takalli jakadiya tana ha'do sabon gumi ta miqa mata jaririyar. Karbar jaririyar jakadiya tayi tana kallonta yanda take canyara kuka ta qura mata ido tareda sauke nannauyar ajiyar zuciya tamiqawa masu gyarata ta fita tana tattaro kuzari ta iso gabansu sultana ta tsaya tareda sunkuyardakai tace, Allah yaqaramiki hkr da lafiya uwar 'dakina Allah ya albarkaci yarima da samun 'YA MACE. Wata irin 6oyayyar ajiyar zuciya sarauniya adama tasauke zuciyarta na cika da wani irin farin ciki amma afili kallon dakinda suhailat take ciki tayi tace, Akimtsa uwar da 'yar amaidasu sashensu Jaririyar akawomin ita nizan kaiwa sultan. Sultana ganin adama tayi mgn yasa ta 'dagawa jakadiya kai tareda cewa jakadiya akula sosai da suhailat ta juya ta fice kuyanginta na bayanta. Lokacinda labarin haihuwar yagama isa koina sultan baice komaiba yace akaiwa maheer 'yarsa yayi mata huduba. Bayan maheer yayi mata huduba aka maidawa sultan 'yar yasa mata suna AMATULLAH. Ba laifi anyi shagalin suna duk wani gata anunuawa suhailat da 'yarta duk da dai tana saneda ba wani farin ciki kowa keyi da haihuwar ba. Adama kuwa sbd jin dadin ansamu mace ba namiji ba har wani soyayya take nunawa amatullah. Watansu 'daya maheer yakoma itakuma ta tafi Mali ganin gida kafin daga can takoma Georgia tasamu maheer. Bayan komawarsu suka cigaba da rayuwarsa cikin kwanciyar hankali kuma sosai maheer keson amah 'dinsa sbd yarinyar babu abinda tabaro nasa na kamanni shiyasa koyaushe take sake shiga ransa. Ta bangaren suhailat kuwa saidai tacigaba da sawa kanta dangana da hkr saidai tunda yanason 'yarta hakan naqara saka mata nutsuwa da kwanciyar hankali. Tunda suka koma cikin dubaru sultana ke 'Dan lurarda suhailat akan kada tayi family planning. Tunda suka dawo yamaida hankali ga rayuwarsa yamanta da wani batun samun magaji da sultan keso. Shekarar amah 'daya da sati biyu aka sake tabbatarda ciki jikin suhailat nan aka sake shiga 'doki da duqufa addua da sadakoki akan Allah yabiya buqata. Wannan karon saida cikin ya tsufa sultan yasa suka dawo akaro na biyu ranar naquda akayi jigum jigum jiran tsammani Allah mai yanda yaso tasake haihuwar 'ya mace. Ita kanta suhailat tayita adduar Allah yabada 'da namijin sbd tafara hangowa kanta da 'yayanta kyara nan gaba. Kai tsaye sultan yace kar akawo masa jaririyar akaiwa maheer yayi mata huduba da suna gabaki daya. Yarima yayiwa 'yarsa huduba yasaka mata suna fammah. Wannan karon babu wani shagali ganin haka yasa yarima ya tattarasu suka komawarsu. Shekarar fammah daya da wata uku suhailat tasake samun ciki wannan karon ma sultan bai cire raiba yace sudawo Satinsu biyu da dawowa ta haifi mace amma 'yar kwana biyu da haihuwa ta rasu ganin haka suka komawarsu sbd wannan karon Sam ita suhailat yanxu ta rage jin dadin masarautar sosai sbd sultana ce kawai ke qaunar 'yayanta sai adama dake yimusu soyayyar dole. Ayanxuma tana 'daukeda ciki tsoho sultan yace suyi zamansu harsai ta haihu anji me ta haifa saigashi ankuma samun mace shine sultana taje tafada masa. Ganin wankin hula na Neman kaisa dare yasa ya yanke hukuncin yarima zaidawo gida atara masa barori koda za'asamu qaruwar ta hanyarsu. Basu dawo Ethiopia ba Mali suka wuce acan gidansu suhailat sukai hutunsu na kusan sati biyu cikin jin dadi sbd gidansu gidan wayayyin mutane ne masu ilimi gasu amah ma sunason nan 'din sbd suna sakewa sosai ga qaunarsu da Granny's dinsu suke musu. Daga Mali komawarsu sukayi Georgia tareda yaransu sukaci gaba da rayuwarsu. Maheer duk cikin yaransa uku babu kamar amah acikin ransa yana tsananin qaunarta Wanda suhailat ke adduar Allah yasa ko kwatankwacin rabin qaunar dayakewa amah tasamu daga garesa. Maheer da family dinsa wata irin rayuwar turawa ta jin dadi sukeyi babu damuwa babu takura. Yaransa sun taso cikin turawa da yanayin rayuwar turawa dasuka ga iyayansu aciki yanayin fatarsu dakeda sirkin yellow da brown kawai zaka zaka kalla kace musu black Americans batareda kasan asalinsu ba. Baby AMNAH Nada shekara biyu tasake samun ciki wannan karon yazo mata da laulayi da nauyin jiki sosai shiyasa ta rage fita aiki sosai dakuma kula da gidan ta 6angare 'daya ga amnah babu lafiya yarinyar tun tana jaririya take fama da pneumonia Wanda idan ya tashi yana wahalarda yarinyar sosai hakan yasa iyayenta ke tsananin qaunarta. Yau tun safe jikin nata yatashi sosai sbd kwana tayi yau bada sweater da socks ajikintaba. Koda Carolina ta shirya amah da fammah shirin zuwa school sukai breakfast Amah ta nufi hanyar palon dadynsu da gudu tana cewa, Dady we're running late pls come out. Fitowarsa daga wanka kenan 'daureda White towel yajiyo muryar amah 'din ya lumshe ido ya bude yakalli agogo yana cewa, Amah will kill me today for this. Kallon suhailat yayi data fito daga dressing room 'dinsa daukeda kayanda sabon towels guda uku zata kai toilet yace, Ki taremin ita na shirya zata cikamin kunne ne da surutu nakasa shiryawa. Aje towels din tayi bakin king size bed din dake cikin qaton hadadden bedroom din nasa ta nufi qofa tana cewa, Amah nima wlh bazan iya da surutunki ba. Tana fitowa amah na kama handle din dakin. Kamo hannunta tayi tana cewa, Let's go and check on amnah before your dad comes out.... Tsayawa tayi tareda 6ata fuska zatayi kuka Suhailat tayi saurin janta suka nufi room 'din yaran dake tsare dakomai na yara. Saurin isa tayi gurin amnah dake kwance agadonta tana fusgar numfashi daqyar. Daukarta tayi da sauri tareda dubata taga ciwontane yatashi cikin karaji ta qwalawa Carolina kira jikinta na rawa. Da hanzari Carolina ta iso tana cewa, Yes ma'am. Cikin daga murya rai amatuqar 6ace tace, Are you trying to kill my poor baby by letting her sleeps without any sweater and socks? Arikice takalli suhailat cikin rudewa tace, I'm sorry ma'am but I....... Just shut up I don't want to hear your stupid silly excuses Hw can you be so careless and..... Keep quite suhailat''''' sukaji daga bakin qofar dakin ta juyo takallesa cikin takaici tace, Baby pls..... I said keep quite suhailat"" yasake fada yana kallon yanda Carolina ke sheshekar kukan fadanda suhailat tayi mata yace, Why do you always wants to make things worst? Yanxu kinxo kinsamu halinda amnah take ciki instead kiyi saurin bata taimakon gaggawa kintsaya hayaniya and you seriously know hw much I hate that, Ga yara basu wuce school ba kinanan kina fada kinkasa tsayawa kiji wat was trying to say. Hawaye ne yaciko idon suhailat takallesa lokacinda ya juya yafice yana zuwa palo su amah suka bisa mota suka shiga ya wuce yafara ajesu school ya nufi gurin aikinsa. Bayan fitarsa share hawayenta tayi ta miqawa Carolina amnah tace, Quickly remove her pampy and dress let me go and change we're taking her to the hospital. Lokacinda suka fito tuni jikinta yaqara rikicewa tun a mota takirasa. Tsaye suke ya zuba dukkanin hannuwansa a aljihun trousers dinsa fuskarsa sai wani irin kwarjini da glowing takeyi sbd kyan fata da hutu yana sauraron bayanan wasu new doctors da aka kawo asibitin wayarsa tayi ringin yakalli nurse din dake tsaye riqe da kayansa na theatre da wayarsa tareda wasu folders din patients din dazaiyiwa aiki ya miqa mata hannu ta miqo masa wayar yana ganin suhailat ce ya rufe idanu ya bude tareda dauka yana komawa office dinsa na qurya. Sanin bayason hayaniya da tashin hankali yasa ta daidaita nutsuwarta tareda share hawayenta tana 6oye kukanta tace, Baby my amnah is leaving me wlh I can feel it.... Rufe ido yayi ya bude Wanda yazamo 'dabi'arsace yin hakan duk zaiyi mgn sbd tattaro maganar kasancewar baifiyason dogowar magana. Jikin ne? Eh baby kwata kwata she's not breathing she's loosing it.... Bring her to hospital yanxunan. Muna hanya already. Kashe wayar yayi tareda mayar da hannuwansa aljihu ya rufe ido. Suna isowa akayi gaggawar fara bata taimakon gaggawa ta hanyar saka mata oxygen saidai tariga tayi nisa sosai mintuna talatin da zuwansu Allah yakarbi ranta. Cikin jinjina alamarin doctors din dake kanta suka gama rubuce rubucensu tareda kallon maheer da suhailat ke jikinsa tana kuka sukace, Sorry doctor maheer we lost her. Wani irin kuka suhailat tasaki tana qanqamesa Rintse idanuwansa yayi ya rungumeta yana bubbuga bayanta batareda yace komaiba. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *9* Bayan rasuwar amnah sosai suhailat tashiga damuwa shikuma gashi bai iya ya ake lallashi ba bare Iyakacinsa idan zai fita yanasaka yin breakfast idan yadawo suyi dinner sbd bai cika lunch agidaba. Hakadai ta dangana tacigaba da rainon sabon cikinta. Sultan yayi yayi yaqara aure yamaqi dawowa qasar shiyasa yadauki mataki kaitsaye akansa. Sultana tashiga damuwa matuqa jin amnah ta rasu batareda sun ta6a ganinba saidai a hoto kawai gashi tanason zuwa amma sultan yasa doka. Jakadiya kuwa sosai tafara shirya shiryen na kullum tana sashe sashe duddubawa cikin dubara sbd sotake saita ringa fahimtar halayyarka sbd kar asamu magaji ta macenda batada nutsuwa ko ma'ana. Kullum cikin kwantarwada suhailat hankali sultana take hardai taga ta warware itama hanakalinta ya kwanta. Lurada jakadiya sultana tayi ta kalleta bayan ta kori dukkanin bayinta dake sashen sbd maganar datakesonyi da jakadiyar. Rumanah ce kawai a bedroom din ammyn tana aikinta hankali kwance. Cikin muryar bada umarni tace, Inason sanin hukuncin da sultan ya yanke akan maheer sbd nasan me shirunsa yake nufi. Sunkuyar dakai jakadiya tayi wani zufa ya tsatsafo mata cikin sanyin jiki da sanyin murya tace, Sultan yabada umarnin atanadarwa yarima sa dakoki har biyar akillacesu zai dawo bazai komaba yanxu sai ansamu qaruwa daga garesu. Tashi zaune sultana tayi cikin wani irin yanayi na tsananin damuwa da takaici taringa maimaita innalillahi. Kallon jakadiya tayi tana qoqarin ganin damuwarta bata rinjayetaba murya amatuqar sanyaye tace, Har kin tanadesu 'din? Tukunadai ranki ya Dade saidai nima ina cikin tsananin fargaba da tsoron yanda zata kaya sbd aurensa ma ta yaya akasamu yayi bare yanxu mata har biyar. Rintse idanu sultana tayi tareda budesu jajir tace, Idan kin zabesu kafin ki gabatarwada sultan su ki gabatarmin dasu inason naga matanda wasu daga cikin jikokina zasu fito ajikinsu. Jakadiya na fita ta bada umarnin abuga qararrawa atara mata dukkanin wata kuyanga dake masarautar. Nan tafara dubasu cikin layi harbasa qirguwa sbd yawansu amma takasa samun 'daya dazata ware duk wadda takalla saitaga komai gyara da kulawar daza'ayi mata batakai matsayinda yarima zai hada shimfida da itaba. Da haka ta sallamesu tace gobe kowanne yayo wanka su sake zuwa subi layi. Tana gama gyaran bedroom din tafito tazo gaban sultana ta durqusa cikin girmamawa tace, Ammy nagama kinada buqatar wani abu? Kallonta sultana tayi da idanuwanta dasukai jajir sbd baqin ciki ta girgiza mata kai. Ganin halinda ammyn take ciki yabata tsoro ta miqe hartakai qofa ta waiwayo cikin damuwa murya asanyaye tace, Saida safe ammy. Asanyaye ta isa dakinsu ta tararda daga mamani har nuratu basu dawoba ta tube taso watsa ruwa amma jin batada gajiya kuma batai wani aikin wahalaba tayi kwanta. Tana qoqarin juyawa nuratu tashigo amatuqar gajiye ta zauna bakin 'yar katifarta tana cewa, Rumanah wlh tsufa da wuri zai kamani sbd wahala. Murmushi rumanah tasaki ahankali kafin ta tashi zaune tace, Me kike gudu da tsufa da wuri? Harararta nuratu tayi tana zame kayanta tace, Ke kuma mekike yiwa sauri da tsufa? Nifa rumanah banason tsufa da wuri sbd bazan ta6a cire rai daga hangowa kaina wata irin kyakkyawar rayuwa, Ke nifa har mafarki nakeyi nazama wadda tafi kusanci ga Wanda wai zai mulki masarautarnan anan gaba, Kuma kinsan menene? Mace nake gani amafarkina koda yaushe saidai adon zinarai dake jikinta tana hanani ganin fuskarta.... Mamani dake shigowa tayi saurin qarasowa ta riqota tana washe dukkanin haqoranta tace, 'Yarda zaki haifawa yarima ce...... Fusgewa nuratu tayi da qarfi tana cewa, Barni da zancenki mamani koyaushe bakinki baya tsayawa mmatsayinsa.. Sake washe baki mamani tayi tace, Nuratuna dama nasan tuntuni jikina nabani kece zaki fitardani cikin wannan qasqantacciyar rayuwar, Jikina nabani kece za'a zaba amatsayin sa 'dakar yarima..... Dariyace taxowa rumanah tayi saurin rufe baki sbd gudun masifa da balain mamani dazata iya kwana tana surfa mata. Cikin takaicin halin mahaifiyarta nuratu takalleta tace, Lallai mamani bakya sona tunda harkike fatar nazama baiwarda za'a riqa kwana dani ina haihuwa ana karbe 'yayan. Cikin saurin mamani tace, Kibar maganar baiwa daga ranarda kika hada shimfida dashi kintashi daga baiwa sbd duk Wadda ta haifo magaji sultan ya 'yantata daga ranar kuma ita za'a miqawa matsayi dakuma kujerar zaman uwar sarki sbd tariga ta haifo sarki, Duk Wanda taso nadawa yayiwa danta riqon qwarya shi zata nada har 'danta ya girma abasa kujerarsa, Idan kika haifi namiji nuratu babu Wanda zaki bawa riqon kwarya kece zakiyi mulkin da kanki, Kece zaki hau kujerar sarauta da kanki, Kece zaki mulki dubban 'daruruwan sarakuna da daulolinsu, Kece zaki zama mace ta farko dazatayi mulkin wannan masarauta da aka tsani haihuwar mata..... Kasa riqe dariya rumanah tayi tasaketa tana kallon mamani data watso mata mugun kallo tayi saurin hadiye dariyar. Nuratu ma dariyar tasaki tana kallon mamani kafin takalli rumanah suka saki wata dariyar. Mamani tayi mugun hasala tayo kan rumanah nuratu tayi saurin riqota tana cewa, Haba mamani nah kece fa uwar sarauniya nuratu kuma kakar magajin sarautar dariyafa kawai mukeyi ta farin cikin wannan mafarkin naki mai dadin gaske kokuwa 'dayar mamar magajin sarauta. Dariya suka qunshe suna kallon juna suna kallonta. Ganin sun maidata mahaukaciya yasa qyaci ta fice ahasale. #Mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *10* Bayan fitarta rumanah taja abun lullubewarta tana murmushi tace, Nuratu kinfa karyawa mamani gwiwa daga kawai tana mana fatar samun jin dadi da 'yanci idan kika zama sarauniya.... Kallonta nuratu tayi cikin tsananin sanyin jiki tace, Rumanah ke kinamin fatar nazama baiwarda za'a riqa kwana da ita tana haihuwa Ana karbe yayan idan nazama haka me naqaru dashi arayuwata bayandai ta tabbata naza baiwa tahar mutuwa... Qarasowa da sauri rumanah tayi ta rungumeta ganin hawaye na zubo mata tace, Nuratu bana miki fatar wannan rayuwar ko amafarki bare afili, Keda mamani kune 'yan uwana kullum fatana da adduana musamu kubuta atare mukoma ga asalinmu domin kuwa saimun koma asalinmu zangano nawa asalin. Cikin sanyin murya nuratu tace, Rumanah bawa baida ra'ayin kansa ko abinda yakeso sai Wanda uwayen gidansa suka yanke akansa, Shin kina tunanin qaddara zata iya zuwa kaina aza6eni cikin masu zuwa shimfidar yarima? Girgiza mata kai rumanah tayi cikin son qarfafata tace, Insha Allah bazamu ta6a wannan rayuwarba nuratu. Rumanah ammy bazata ta6a bari kiyi wannan rayuwarba saidai ni banada tabbaci saidai Allah ya dubi rashin gatana. Jiki sanyaye zuciya fal da tunani da zullumi suka kwanta har mamani tadawo cikin dare ta kwanta babu Wanda yayi bacci acikinsu sbd tunani. Washe gari fuska 'daure mamani ta tashi babu Wanda ta amsa gaisuwarsa acikinsu qarshema kan rumanah taso sauke haushinta Dan har marinta tayi daga gaisuwa. Cikin sanyin jiki ta share hawayenta tareda girgizawa nuratu data bude baki zataiwa mamani magana kai tareda sakin murmushin dole mai ciwo kafin ta kammala shirinta ta fice tana cewa, Natafi'"""cikin sanyin murya. Kodata isa sashen part ammy cikin sanyin jiki tafara aikinta har qarfe goma tabuga lokacin ammy ta tashi Kanta qasa tagaida kafin tahau gyaran dakin cikin rashin walwala da rashin kuzari sbd duk lokacinda mamani tayi mata Abu abin na taba zuciyarta ganin batada wasu 'yan uwa kamarsu tunda sukadaine nata. Ammy sosai ta lurada rashin walwalarta ta danne tata damuwar cikin kulawa takira sunanta. Amsawa tayi tareda barin gyaran gadon datakeyi tazo gabanta ta durqusa kanta na qasa. Qare mata kallo tayi taga yanda jikinta ke 'Dan rawa tace, Rumanah meya faru dake? Mayarda hawayenta tayi cikin qarfafa muryarta tace, Bakomai ammy. Sam batason takurawa rumanah shiyasa ta kyaleta kawai. Tundaga lokacin sabuwar tsangwana da muguwar tsana tashiga tsakaninta da mamani sbd gani takeyi itace take zugewa nuratu kunne akan tadaina wanka da tsafta sbd kar azabeta. Duk yanda take daurewa kasawa takeyi saita kwana tana kuka sbd wani irin zagi da gori data sakota gaba dashi akan iyayenta dasuka rasu. Tun tana boyewa tuni damuwa tabayyana ajikinta sbd ramar datayi. Sultana duk datana cikin damuwar dawowar maheer dakuma hukuncin sultan Saida damuwar ganin halinda rumanah take ciki tadameta musamman ganin tana ramewa ta daina walwala kwata kwata ta mayarda kanta cikin bayi 'yan uwanta duk wani aikin wahala tanayi Wanda yaqara hargitsata. Duk yanda sultana tayi da ita tafada meke damunta ta nuna mata ba komai sbd idan tafada tasan azabardasu mamani zasusha zai iya sanadin rayuwarsu kuma bazai tsaya akantaba harda nuratu. Jakadiya itace ta bincikowa sultana tsaf abinda ke faruwa da rumanah sosai ranta ya 6aci hartayiwa sultan Aiken abinda ke faruwa da rayuwar 'yar amintaccen bawansa daya rasu saikuma ta dakatar sbd tasan hukuncinsa bazaiyi dadiba Dan rayuwarsuce ke lilo a sama kuma barinsu duniya tamkar barin asalin rumanah ne sbd mamani kadaice tasani. * Qarfe biyar na yamma jirginsu ya sauka a qasar Kasancewar ansan bayason rawar jiki da yawa yasa motoci uku kawai sukazo daukarsa da iyalinsa sai khaleefa dasuka zo tare bayan yazo gurinsu daga zuwa weekend yabiyosu suka dawo tare. Tunda yafito ake zubewa ana gaishesa so daya kawai yadaga kai alamar amsawa hannunsa daya na aljihun wandonsa sai shades dinsa daya gyara. Suhailat na gefensa ta saci kallonsa zuciyarta na nauyi sbd ganin tsantsar kyawu da kwarjininsa taji kishinsa na taso mata tayi saurin dauke kai tana gyara riqon handbag dinta. Itada shine a mota 'daya 'dayar motar khaleefa dasu amah sai 'dayar ta guards. Koda suka isa masarautar tuni duk wani guard da manyan masarautar suka fito tarbonsa. Cikin girmamawa ake zubewa ana gaidasa harya isa gaban mahaifinsa a hankali yasaki murmushin da iyakacinsa fuskarsata ya gaidasa sultana cikeda girmamawa da kewarsa. Lokacinda isawarsu maheer ta isowa sultana sakin murmushi tayi cikin tsananin farin ciki kafin tayiwa wanda ya isoda saqon babbar kyautar yana ficewa suhailat dasu amma suka shigo part 'din jakadiya na gaba. Cikeda girmamawa suhailat taqaraso gaban sultana ta durqusa duk da cikinta daya fara girma ta gaidata. Cikeda kulawa sultana ta amsa tana kallonsu amah dasuka zauna jikin mahaifiyarsu sbd rashin sabo dasu. Tana kallon yaran tace, Jakadiya aje asake dubowa part dinsu idan gyaran ya kammala sbd yaran sun gaji suna buqatar hutawa. Washe baki Jakadiya tayi cikin girmamawa tace, Allah yataimaki sarauniyar sarki kuma kakar sark ai tun asubar fari baiwa rumanah ta kammala duk wani gyara da'akasata a part 'din daga part 'din na yarima har part din gimbiya suhailat kuma kuyangi biyar nacan najiransu domin hidimarta data yara kuma anyi musu gargadin ko kallon part din yarima karsuyi bare tunanin shiga koda dasunan wanine ya aikesu. Murmushi sultana tasaki tareda kallon suhailat tace, Suhailat kuje kuhuta da yaran sun gaji sosai. Miqewa tayi daidai fitowar rumanah daga bedroom din ammyn fuskokinsu suka sauka akan na juna daidai kuma shigowar yarima a palon na qurya Wanda qamshinsa yasasu juyawa qofar atare. Saurin durqusawa rumanah tayi tareda sunkuyar dakanta ta gaidasu atare batareda ta bambamtaba. Suhailat ce kawai ta amsa cikin wani mugun sanyin jiki daya saukar mata lokaci 'daya. Ammynsa ya nufa da wani irin murmushi da duk duniya itakadai yakewashi Cikeda farin ciki da murmushin daya kasa 6oye farin cikinta ta miqe tsaye yana zuwa ya rungumeta. Cikin rawar jiki rumanah ta fice sbd wani kallo da Jakadiya ta watso mata. Itama jakadiyar ficewa tayi hakama suhailat sbd tasan qaidane idan zai gana da mahaifiyarsa kowa ficewa yakeyi sbd itakadaice takejin doguwar maganarsa bayan ita ko suhailat datake matarsa baya doguwar magana da ita,su bayi ma ko masu hidimarsa tun tashinsa bayajin yata6a yiwa bawa magana. Bayan fitarsu Jakadiya takalli rumanah data nufi qofar fita babban palon farko tana qoqarin barin part din gabadaya takira sunanta. Dawowa tayi tana sunkuyar dakai sbd ko iya dagowa takalli suhailat bata iyayi sbd faduwar gaban datake ji. Ki kama yaran ki rakasu part dinsu ta huta akula da yaran kar abari su dameta sbd yanayinta. Jinjina kai tayi cikeda ladabi ta miqe ta 'dauki fammah tareda riqe hannun amah kuma ta 'dauki handbag din suhailat din tabi bayanta. #Mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *11* Suna isa part din na suhailat dake kallon na yarima itace tayi saurin matsawa ta bude mata qofar tashiga. Babban parlour ne daya tsaru sosai da uwayen nairorin da aka zuba masa gurin tsarasa, Royal cushions ne purple and golden komai na palon qyallin adon kalar golden din. Duk haduwa da tsaruwar part din sultana saidataga wannan ma na suhailat yayi kyau sbd ita atunaninta baza'ataba samun part dinda yakai na sultana tsaruwa da kyauba saigashi na suhailat dinma ya tsaru kamarna sultana duk da tanajin labarin haduwa da tsaruwar part din adama kasancewarta itama 'yar adoce sosai. Kuyanginda aka turowa suhailat 'din sukayi saurin shiga taitayinsu suna mata barka da shigowa. Hannu kawai ta 'daga musu tareda kallon rumanah tana nuna mata 'dakinsu amah tace, Kije kiyi musu wanka da ruwa marasa sanyi kuma bamasu zafi sosaiba ki shiryasu sai abarsu su huta kafin anjima suci abinci. Tana gama fadar haka tamiqa mata hannu ta bata handbag dinta ta shige bedroom dinta. Dakinsu ta nufa dasu tayi musu wanka ta shiryasu harzata fito suka maqale mata takaisu gurin mum dinsu. Bata saba da yaraba batama ta6a zama da yaraba tun tasowarta Daqyar tasamu ta lallabasu ta fito. Tana fitowa part din tasaki ajiyar zuciya sbd gabadaya a takure take sbd tsoro da gudun aikata laifi. Kodata koma part din sultana a palon farko ta ra6e sbd ganin alamun har lokacin yarima naciki. Gab da magrib yafito tayi saurin zubewa amma ko lurada akwai mutum shibaiyiba ya wuce yabar part din da qamshinsa. Sum sum ta nufi palon ciki ta tararda ammyn zaune har lokacin ta durqusa cikin girmamawa tace, Ammy a table za'a jera abinci kokuwa anan? Murmushi tayi cikeda farin ciki tace, Ajera a table kuma ayiwa maheer honey pancakes da sugarless drink sbd bayacin abinci mai nauyi musamman yanxu da daddare And kihada masa fruitsalad with less apple sai kikai masa part dinsa kisaka a fridge din Palo nasan idan yafito sallar magrib bazai komaba sai dare. Wani irin yawu ta hadiye na muguwar faduwar data sameta jin inda aka aiketa itadai batason tayi laifi komai qanqantarsa. Ficewa tayi tafara kawo abinci a second palo tana jerawa a dining jikinta amatuqar sanyaye. Honey Pancakes din tayi tareda kawowa dining daidai lokacin aka shiga sallar isha takoma tahado fruit salad ta zuba a glassbowl ta 'daura a tray ta nufi part 'dinsa qafafuwanta har wani hardewa sukeyi sbd yanda jikinta ke rawa. Tana isa kallo 'daya tayiwa guards din qofar ta juya tayi part din suhailat ta saka cikin fridge tareda sanarda kuyangin palon su sanarda suhailat ankawo fruit salad din yarima. Kodata koma sallah taje tayo tareda komawa part din sultana tana saka kai da sallama dashi idanuwanta suka faracin karo yana cin pancakes din yana yiwa mahaifiyarsa murmushi. Juyawa tayi da sauri sultana ta lurada ita amma sanin bayi basa zuwa idan yana guri musamman idan abinci yakeci kozaici yasa tabarta takomawarta. Sai qarfe tara yabar part din sultana yanufi nasa Yana zuwa ya tu6e yashiga bathroom dinsa da aka cika masa bathtub da ruwa masu matuqar qamshi da 'dumi ya lumshe fararen oily eyes dinsa tareda kwantawa yana sake jin nutsuwa. Allah yayisa mutum mai tsananin son rayuwa musamman tajin dadi saidai suhailat bata cika son irin wannan rayuwarba itakuma sbd sunada abubuwan dasuka banbanta ra'ayoyinsu saidai suna qoqarin ganin hakan baitaba rayuwar aurensuba. Sam bayason wanka a shower saidai a bathtub sbd yafison koyaushe yakwanta cikin ruwa tsawon mintuna goma sha biyar zuwa ashirin kafin yayi wanka, Itakuma suhailat Sam batason wanka a bathtub saidai shower shiyasa haryau baisamu irin rayuwarda yakesoba sbd basu ta6a wanka atareba Kwata kwata batama shiga toilet din bedroom 'dinsa sbd 'duk girma da fadin toilet dinsa bayason ganin ruwa ko yayane a qasan toilet dinsa itakuma idan tashiga toilet saita gama jiqa koina take fitowa. A bangaren rayuwar aurensu kuwa Sam bata iya kwana a 'dakinsa sbd komai dare idan suka gama abinda sukeyi a bedroom dinta take kwana sbd daga ita harshi kowa yafison ya kwana shikadai akan gado shiyasa yawanci zata raba dare a bedroom dinsa susha love dinsu kafin tayo dakinta. Bayan sun jima da aure yazo yasaba baya iya kwana sai ajikinta amma itakuma dukkanin cikin datakeyi bayason kwanciya dashi hakadai yama cirewa ransa kota haihu basa kwana tare saidai su raba dare tare. Bude idanuwansa yayi ahankali tareda kallon ruwan sbd qamshin dasuke fitarwa yakalli gaban mirror din cikin toilet din yagansu kaloli kusan guda goma masu kalar qamshi dabam dabam. Saidayayi mintuna kwance cikin ruwan kafin yayi wanka ya fito daureda brown towel sabo qal ya tsaya gaban mirror tareda goge jikinsa ya fesa Hugo black men's spray tareda gyara sumarsa da lafiyayyar qasumbar dake kwance a farar fatarsa fuskarsa ya fesa mouth spray mint flavour ya nufi closet ya dauko kayan bacci white colour yasaka tareda nufar makeken lafiyayyan royal bed dinsa dayake gyare da komai white da kusan eight pillows masu laushi. Wayoyinsa ya kashe tareda ajesu a bedside drawer ya kashe wuta yabar bedside lamps masu duhun haske. Kwashe komai tayi tasake gyare palon tayiwa ammy Saida safe ta nufi gefensu na bayi anatse. Tana zuwa babu kowa a dakin ta kwanta bayan tacire uniform dinta tasaka tsohon uniform dinta sbd sune tamayar na bacci dama idan akaga uniform dinka sun mutu ana baka wani. Kodasu mamani suka shigo idonta biyu amma ta lafe tanaji mamani nata fada tana zaginta Ta share hawayenta tareda rufe ido tana danne kukanta. Tundaga ranar kusan itace take wahala da suhailat da 'yaranta sbd kullum ita sultana ke aikawa tana yiwa yaran wanka takuma kaimusu abinci ta Jere a dining safe rana dare saiya zamto ayyuka sunmata yawa danma babu laifi suhailat na sakar mata fuska sosai hakama yaran ba laifi suna yarda da ita ba kamar kowaba sbd kullum ita ake sawa ta daukosu takawo gurin sultana su yini kokuma gurin sarauniya adama. * Sati 'daya da zuwansu yarima yana zaune gaban sultan sbd kiransa dayayi cikeda girmamawa yake sauraren mahaifin nasa. Cikin iko da umarni sultan yace, Aure zaka qara maheer ibn abdulshams. Shiru yarima yayi cikin tsananin mamaki tsawon lokaci harsaida mataimakin sultan yasake maimaita masa kafin ya 'dago manyan oily eyes dinsa yakalli haris abdallah mahaifin khaleefa kuma mataimakin sultan yace, Ina bawa sultan da mataimakinsa hkr sbd babu sha'awa ko burin qara aure arayuwata. Wani shu'umin murmushi sultan yasaki tareda sake maimaita zancensa. Shima maheer cikin girmamawa yasake maimaita amsarsa. Kallonsa sultan yayi yasan sarai waye maheer saidai bazai barsaba zaiyi amfani da qarfin ikon mulkinsa dakuma ikonsa na mahaifinsa akansa. Batareda yakallesaba yace, Maheer ibn abdulshams zabin farkone nabaka na qarin aurenka. Rufe idanuwansa yayi ahankali yana danne 6acin ransa yace, Ina qara bawa sultan hakuri akan wannan buqatar tasa sbd idan nayi auren bansan yaya zan iya kwatanta adalcin kulada mata biyu ba. Murmushi sultan yasake saki tareda kallon sarkin gida dake tsaye da sauri yafice ya nufi hanyar part din sultana. Mintuna qalilan akayiwa Jakadiya iso tashigo tareda zubewa qasa tana gaisuwa. Cikin mulki da nuna ikonsa yace, Jakadiya aje yau awanke masa baiwar datafi kowace kyau 'daya cikin biyar 'din danace agyara akai masa daga yau aringa kaita kowane dare harsaitayi ciki, Kuma daga yau an dakatarda matarsa zuwa gurinsa sai baiwarsa tayi ciki Idan ya kaucewa umarnina Jakadiya ki sanarda sultana zaarah na sauketa daga matsayinta na sultana kiyiwa adama albishir da samun sabon matsayi. Yana fada ya miqe nan dukkanin su haris abdallah suka miqe yashigewarsa palonsa na musamman. Cikeda girmamawa Jakadiya tace, Angama sarki mai adalci. Miqewa tayi da sauri ta fice sbd ganin halinda yarima yashiga sbd tsananin 6acin ransa da baqin cikinsa daya kasa 6oyuwa. Miqewa yayi yafice kai tsaye part dinsa ya nufa tareda bawa guards din qofar part dinsa gargadin duk Wanda yayi motsi mai qarfinda harzai shigo part dinsa yadamesa arufesa tsawon shekara guda. Jin haka yasa akayi sanarwa tuni kowa ya nutsu yashiga taitayinsa. Jakadiya kuwa cikin qanqanin lokaci tasa aka tara dukkanin wata baiwa dake masarautar mai shakatun dabasu wuce sha takwas,sha tara zuwa ashirin da uku da hudu. Koda aka kira duk suka halarta banda rumanah dake bedroom din sultana tana jera kaya acikin closet. Duk iya damuwa da rashin mafita sultana naciki sbd tun binciken farko Jakadiya tace bataga wadda ta daceba gashi sultan yace yau. Zaune kawai take amma hankalinta nakan halinda maheer yake ciki yanxu. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *13* *_JAN HANKALI_* *_'Yan uwa masu zantuka akan wannan littafi masu dadi da marasa dadi tareda cin fuska duk inason Ku luradafa_* *_akowane lokaci mai rubutu idan zai isarda wani saqo na halin rayuwa tofa dolene saiya fara kawo 6atancinsa da 6arnarsa kafin yazo ga darasin ciki tareda gyaransa Dan haka please muriqa bari muna ganin inda aka dosa kafin muriqa fadar ra'ayoyinmu._* *Not edited* Komai bakinta baida kuzarin furtawa koda yanadashi 'din baida ikon furtawa sbd hakan na nufin ruwan sama zai wanke jininta bayan anraba jijiyoyin dasuka riqe kanta da wuyanta Saidai bazata iya hana zuciyarta qunci da radadin zuciya ba sbd sai ayaune ta sake tabbatarda ita baiwace Mara 'yanci gaba da baya. Kai tsaye part din gyara taga sun nufa nan shakkunta da wasi wasinta ya tabbata kenan itace zata zama..... Kasa qarasawa tayi ta rufe idanuwanta da qarfi hawaye na 6alle mata. Daganan kasa daga kafafunta tayi haka suka jata kamar makauniya suka shiga da ita. Zaunarda ita sukayi tareda fara zame mata kayan jikinta har lokacin bata iya 'daga koda Dan yatsanta bare ta iya 'dago fuskarta. Shigowa Jakadiya tayi kallo daya tayi mata tagano tsananin dukan da firgici yayiwa zuciyarta tayi saurin dauke kai cikin bada umarni tace, Ku shiryata shirinda har abada yarima zai riqa tuna qamshi da kyawunta kuma Ku kwantarda hankali kuyishi anatse. 'Dagowa tayi ahankali takalli jakadiya daidai lokacin hawayenta suka samu tsinkewa. Cikin zafi da daure fuska jakadiya tace, Karkiyi mana kuka sbd ke baiwace da akeda ikon kwana dake aduk lokacinda akaso kuma akeda ikon yin yanda akeso dake Dan haka ki saurara da kyau Idan kikayi mana garaje anan wlh abincin kaji za'ayi da jininki. Kalaman Jakadiya sundaki zuciyarta matuqa ta rufe idano ahankali ta budesu jajir sbd quncin zuciya amma tabbas babu yanda zatayi ita baiwace kuma yar bayi kamar yanda Jakadiya ta fada Hannu tasa tashare hawayenta bata qara motsiba suka fara aikinsu ganin ta zame rigarta tashiga cikin ruwan madara da lalle dake cikeda bathtub suna zuba qamshi. Jakadiya Juyawa tayi tafice takoma part dinda aka warewa baiwarda duk aka zaba akusadana suhailat yake Saidai baiyi girman nataba. Duk wani abin jin dadi da hutawa da more rayuwa ansaka sbd so ake jikinta yariqa murmurewa fatarta tasamu isashen Hutu da kulawa ta yanda yarima zaiji dadin mu'amala da ita. A cikin bedroom dinda ke part din wardrobe din dakin cike take tab da wasu irin kayan barci marasa kyawun gani basa qirguwa, Hakama braziers masu daukar hankali dakuma panties, 6angaren turaruka kuwa duk wani turare mai tsada da qamshi ansiya har gaban mirror bai daukesuba aka zuba wasu a wardrobe. Suhailat Jakadiya ta tambaya duk wani Abu da yarima yafiso ta 6angaren tayar masa da sha'awa zuwaga auratayya bisaga umarnin sultan, Cikeda damuwa ta zayyanowa Jakadiya shinefa aka nemi turaruka masu matuqar tsada da kayan barci. Saidata tabbatarda gyaran komai yakammala takoma gurinda ake shirin rumanah din ta tarar sungama shiryata cikin wata irin doguwar riga maroon colour dataji wasu irin tsadaddun adon sequence stones sai rawa take tana qyalli. Mayarda kallonta tayi zuwaga fuskarta cikin tsananin mamaki da fargabar zallar kyawunda sultanace kawai take gani da kwatankwacinsa zuciyarta tayi mugun bugawa cikin zuciyarta tace, Ya Allah kabar wannan fuskar mai tsananin kyawu da kwarjini ta dauwama ahaka karka wanke kyawun fuskarnan da jinin bayinka. Cikeda umarni tace, Ku rufeta mutafi daga yau rana bazata qara ta6a fatartaba harsai yarima yagama da ita idan ya gundura da ita, Hakama daga yau idan tafara kwana barayar yarima duk bawa namiji yabari tsautsayi yasashi kallonta anyiwa zakunan fita yaqi alqawarin namansa. Sam bata jinsu sbd damuwa da qunci dayayiwa zuciyarta yawa Haka aka rufeta aka kamo hannunta suka jata. Part din da'aka ware mata aka kaita har cikin bedroom Jakadiya ta kaita ta janye lullubinta tareda kallonta fuskar tamke da kakkausar murya tace, Daga yanxu kinshigo kenan bazaki sake fitaba sai ranarda kika haihu, Daga yanxu dokace mai tsanani babu Wanda yakeda ikon ganinki sai yarima kawai, Akwai komai na buqata kullum dare zanxo narakaki barayar yarima harsai ranarda kika samu ciki saiki fara shiri daga yanxu Zanje bayan sallar ishai zandawo nakaiki yarima baya jira Saidai ajirasa. Ficewa tayi tabi bayanta da kallo idanuwanta na qoqarin cikowa, Kukan datake dannewane tuntuni ya kufce mata ta zame qasa tafara wani irin kuka tana shidewa, Kuka takeyi sosai tana qanqame jikinta cikeda tsoro,fargaba da baqin cikin rayuwardata tsinci kanta dakuma wadda zata fara daga yau bayan anfara kwanciya da ita duk lokacinda akeso. Sbd kuka muryarta shaqewa tayi tashare hawayenta tareda miqewa ta nufi toilet din bedroom din tayo alwala daqyar take gani sbd kumburin idanuwanta da fuskart. 4 hours later. Kasa kallon kanta tayi ta rintse ido jiki amatuqar sanyaye sbd kayanda ke jikinta, Riqar baccice kalar black Wanda babu wani sashe na jikinta da rigar ta suturta, Bra da pant dinda aka sata sakawa duka suma black ne aka daure dogon gashinta dashima aka gyara hatta turaren hayaqi mai wani irin qamshi anyiwa gashinta bare jikinta aka daure tsakiyar kai tareda 'dora mata wata doguwar tiga mai hula data rufe koina ajikinta aka rufe fuskarta da hular tareda bata wasu takalmi masu laushi ta zufa anatse Jakadiya tace, Mutafi,Allah yadatar dake da samun ciki acikin daren yau. Jakadiya ce agaba sai ita abaya bayi kusan guda biyar sun zagayeta suna kama rigarta dake Jan qasa. Duk takunta 'daya kamar zuciyarta zata fadone ta buga sbd bugawa da tsananin tsoro da baqin cikin datake ciki, Akaro na farko arayuwarta zata kwana da namiji ba mijintaba kuma duniya da kowa zasusan ana kwana da ita harta haihu, Tabbas da ubangiji bai halastawa uwayen gijiyoyi bayinsuba da ayau tafison a raba kanta da wuyanta abawa dabbobi jininta data cika wannan umarnin amma sa6a musu da bijire musu tamkar ta bijirewa ma'aikintane sbd shine ya halasta hakan. Wani irin tsaro ne na musamman a part din yarima ga wasu irin hasken fitilu masu kyau da burgewa haka duk fadin masarautar idan kacire uban gayya sultan part dinsane ne kawai mai palo hudu kafin akai master bedroom dinsa. Cak suka tsaya bakin qofar shiga  Jakadiya tajuyo ahankali tayiwa bayinda ke bayansu kallo daya Suka ja baya suka tsaya tareda sunkuyar dakai kafin tajuyo takalli guards din bakin qofar cikin girmamawa suka wangale qofar ta saka qafa tashiga. Wani irin numfashi rumanah tasake sbd kukama yanxu yagaji yagudu yabarta zuciyarta da idanuwanta sun bushe sauke numfashi kawai take yi akai akai sai jikinta dayake wata irin rawa ko Abu bazai iya tsayawa ahannuntaba. Numfashi tasauke ahankali tareda 'daga qafarta tashiga ahankali tareda rufe ido tabude sbd rayuwarta ta canxane daga yanxu data sako qafar palon yarima maheer ibn abdulshams abdallah. Har lokacin fuskarta rufe takeda hular rigar dake jikinta ahankali take takawa faduwar gabanta da rawar jikinta na tsananta harsuka isa palon qarshe Wanda dagashi sai bedroom dinsa. Abakin qofa Jakadiya ta tsaya tareda juyowa tayi mata kallon mintuna uku kafin tazagaya bayanta ahankali tasaka hannu ta zame doguwar rigar mai hula Tasaka hannu ta zare ribbon dinda aka 'daure gashinta Gashin ya zubo kan kafadunta ta juya mata baya cikin sanyin murya tace, Kishiga ki kwanta a gadon dake dakin kijira isowarsa. Shiru tayi tareda Jan numfashi ahankali tasauke sbd barazanar barin qirjinta dayakeyi., Daqyar ta iya daga qafafunta dake rawa Rawa hannunta keyi sosai takasa bude qofar bedroom din Ganin haka Jakadiya ta matso tareda dafata cikin kulawa tace, Karkiyi gardama da qaddara ki nutsu kibi umarni kiyi biyayya Allah ne kawai yasan dalilin komai dake faruwa. Bude mata qofar tayi tareda juyawa sbd batada dama da iko tareda hurumin ganin makwancin yarima. Akaro na farko da wani yayi mata magana da sigar lallashi tun bayan data zamto za6abbiya. Ajiyar zuciya tasauke tareda saka qafarta cikin dakin Jakadiya ta jawo qofar ta rufe ahankali kafin ta juya ta fice da doguwar rigar ahannunta. Komai na 'dakin white and golden ne, Sanyin AC da qamshin dakin da mai dakin tareda nata data shigo dashi suka taru suka sauyawa dakin yanayin qamshi mai dadi kasancewar turarukan arabian oud akayi mata amfani dasu sabanin nasa dasuke designers na turawa. Daqyar qafafunta suka kaita bakin couch dake bedroom din ta sulale qasa ta jingina kanta jikin kejerar tareda rufe idanuwanta. Qarfe goma da rabi yafito part din sultana ya nufi part dinsa guards biyu ba bayansa yana isa masu tsaron qofar sukai saurin budewa yashige. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *12* Akan nuratu jakadiya ta tsayarda idanuwanta tana nazarinta sbd zama da rumanah yasa itama takeda nutsuwa daidai gwargwado...... Tsaya to idan zama da rumanah yasa takeda nutsuwa ba kamar mahaifiyarba me zai hana su dauki Mai nutsuwar gabaki daya. RUMANAH"""shine sunan dayazo ranta atake tasaki murmushi cikin farin ciki sbd tasan sultana idan taji ta inda jikokinta zasu fito bazataji damuwaba. Sallamarsu tayi tareda juyawa kar tsaye ta nufi hanyar zuwa gurin sultan. Tana zuwa akai mata iso cikeda girmamawa ta zube gabansa cikin bayyanarda farin cikinta tace, Allah yataimakeka ansamu baiwa mafi nutsuwa da kyawu acikin bayin masarautar mineelik, Baiwa ummu-rumanah 'yar tsohon aminyaccen bawanka bulama. Shima wani irin murmushi yasaki tareda kallon Jakadiya yace, Allah yayi saina hada zuria da bawa mafi soyuwa agareni Aje ashiryata yau za'a fara rakata turakar yarima Bulama Allah yaji qanka da rahamarsa, Jakadiya kije idan ta haifi namiji ina miki albishir da akwatin dalolin amurka. Miqewa tayi tana zuba godia da farin ciki tareda adduar asamu biyan buqata. Lokacinda ta isa gurin sultana ta zube gabanta ta zauna cikin farin ciki tace, Allah yataimakeki Ansamu wadda nasan zakifi kowa farin cikin fitowar jikokinki ta tsatsonta. Kallon rashin fahimta sultana tayi mata cikin qoqarin Kore damuwarta sbd jin ansamu mafita. Baiwa ummu-rumanah ta wajenki itace nakega tafi cancanta da'a za6a sbd ganin nutsuwa dakuma shakuwar dake tsakani. Wani irin kallo sultana ta jefi Jakadiya dashi cikin mamaki da takaici. Datasan rainon datakewa rumanah na idan tasamu sanin asalintane daga mamani ta 'yantata danta koma gida cikin yan uwanta ne. Dauke kai tayi cikin bada umarni tace, Kije kinema masa wata banda rumanah. Kallonta Jakadiya tayi da sauri cikin mamaki tace, Allah yataimaki sultana naga tafi kowace baiwa cancanta tazamo uwar jikinki koba komai tunda 'danki ne ba wani akace akaiwaba. Girgiza kai tayi tareda juyawa takalli qofar bedroom dinta da rumanah ta fito cikin nutsuwa daukeda zanin gadon data cire ta fice tana mamakin kallonda suka biyota dashi kamar ta canza. Laundry din masarauta ta nufa takai kayan ta karbo wasu sabbin zannuwan gado masu laushi farare qal tana fitowa mamani ta shigo part din laundry din daukeda kayan wankin adama itama takawo. Saurin matsawa tayi tana cewa, Mamani sannu da aiki. Tsayawa mamanin tayi tareda kasa danne baqin cikinta da takaicinta akan rumanah din sbd ko yauma dai ba'a zabi nuratu ba sbd ko wanka batayiba. Cikin takaici tace, Rumanah tunda kika zuga nuratu Dan karmu samu farin ciki kema bazaki ta6a farin cikiba arayuwa, Keda iyayenki kunzamarmin muguwar qaddara sun mutu sunbarmana masifa gashinan kin shiga tsakanina da yata kin shiga tsakaninmu da farin cikinmu.... Rintse idanuwanta dasukai jajir tayi Cikin dannewa tace, Kiyi hkr mamani bawa baya wuce qaddararsa ko....... Shaqota tayi cikin tsananin baqin ciki jitakeyi kamar ta cire takaicin iyayenta na shekara da shekaru akanta ta huta. Hawayen wahala rumanah ke fitarwa sosai batareda tayi yunqurin kwatar kantaba. Motsi yasa mamani sakinta ta kwashi kayanta ta wuce zuciyarta na tafarfasa. Kukan datake riqewa tana shiga bedroom din sultana tasakesa zuciyarta na quna, Sosai take kuka tana shesheka sbd yanxune take 'dandana maraici da quncin dake cikinsa, Wannan karon harcikin ranta takejin qunci da radadin abinda mamani ke mata shiyasa takasa danne kukanta duk yanda taso. Sheshekar kukane yadauki hankalin sultana da jakadiya cikin sanyin jiki suka dubi qofar cikeda tausayawa Jakadiya tace, Sultana amincewa kibada rumanah shine zai sanyaya mata qunci da damuwar datake ciki na  uwar riqonta sbd natabbarda shine zai nesantata daga uquba da tsangwamarta., Koba komai wannan itace iya mafi girman soyayyar dazakiyi mata ta amince mata ta zama mai kawarwa da 'danki sha'awarsa., Har abada rumanah bazata ta6a wulaqantaba idan ta hada shimfida da yarima koda kuwa bata haihuba, Ki qara dubawa sultana. Shiru tayi tareda rintse idanuwanta cikin rashin madafa da shawara sbd bata fatar rumanah tazama baiwarda za'a riqa kwana da ita tana haihuwa ana kar6e 'yayan daga qarshe kuma asallameta tayi nesa da qasar bazata qara kusanto 'yayantaba. Wani 6angaren kuma batada wata mafita ko ba6in daya wuce rumanah din Dan itace taga tafi cancanta da jikokinta su fito daga gareta koba namiji bane itadai gwara ace rumanah 'dince ta haifar matasu ba wata baiwarba Saidai zuciyarta na ganin kamar bata yiwa asma'unta adalcin zaman amincin dasukayiba Hakama zuciyarta na hango mata wani irin rikici da tashin hankali agaba akan hakan. Miqewa tayi cikeda damuwa da fargabar rashin madafa, Masarautarsu has been cursed tun shekara da shekarun dasuka shude, Duk wani abin alkhairi baya 'dorewa a masarautar, Sarakunansu hankalinsu da tausayinsu tareda imaninsu yana gushewa daga lokacinda suka hau kujerar mulkin basa da hukunci saina yankewa duk Wanda yayi laifi kisa, Hannuwa da qafafun sarakunansu na jiqene da jinin mutane, Sarakunansu are posses, Duk Wanda ya alaqantu da kujerar mulkin mineelik sai cursed din yashafesa sbd mugun abin daga kujerar yake., Jakadiya kinsan me zamantowa uwa ga magajin masarautar nan yake nufi, Maheer yaqi karbar sunan magajin sarkine sbd kubutardani daga zamtowa cikin makusanta kujerar mulkin, Yaqi karbar sunan ne sbd kubutarda kansa daga jiqa likkafaninsa da kabarinsa da jinin bayin Allah, Kinfi kowa sanin tarihin masarautar nan da abinda ke bibiyarta shine zamu 'dauko yarinyar da batada hakkin komai musakata da abinda zata Haifa? Rumanah kwaqwalwarta bazata iya daukar masifun dazasu biyo bayan zamtowarta mahaifiyar magajin masarautar nanba, Idan muka sakata cikin wannan masifar muka jiqa hannuwanta da jinin mutane bamuyi mata adalciba, 'Dana yakubatardani da kansa daga wannan masifar shine zamu saka yarinya aciki bayan batasan me hakan ke nufiba., Sultan alamarin yariga ya dade shigarsa ayanxu koda 'Dan cikinsa baya tunani biyu kafin ya yanke musu hukuncin kisa, Masifar tariga tashiga jikinsa bayaji baya gani rashin bin kowane irin umarninsa daidai yakeda fitar ranka.... Cikeda sanyin jiki Jakadiya tace, Hakan zaki tuna kiyi hkr kibada rumanah idan ta haihu mu tseratarda ita ta hanyar turata nesa inda har abada bazata sake kawo kanta nanba wannan shixai mata Katanga daga zamowa MINEELIK-ASSULTANAH TA BIYU. Shiru sultana tayi cikeda tsananin tsoro da fargabar abinda suke shirin yi,. Fitowar rumanah daga bedroom dinta yasasu juyawa qofar. Sunkuyar dakanta tayi sbd fuskarta datayi jajir sbd kukandatayi. Wani irin mugun sabon tausayinta yashiga sultana batasan lokacinda tajawota jikinta ta rumgumeba cikin wata irin sanyin murya tace, Asma'u ki yafemin. Rumanah kema karki qullaceni. Batamaji abinda ammyn kefadaba sbd kukanta daya dawo sabo tuntuni take Neman Wanda zai rarrasheta koda tsuntsune sbd mawuyacin halinda take ciki. Jakadiya ma cikin tsananin tausayin rumanah din can qasan maqoshi tace, Ki gafarceni rumanah amma rayuwarki ta birkice daga lokacinda kika haifi 'da namiji sbd qaunar danake yimiki ina miki fatar samun 'ya mace sbd kubuta daga muguwar tsinuwar dakebin makusanta kujerar masarautar mineelik. Saida rumanah tayi kuka sosai Wanda hakanan yake zuwa takasa tsaidasa saidatayisa sosai kafin sultana ta 'dagota tareda kallon fuskarta tana maida hawayenta takalli jakadiya tareda 'daga mata kai ahankali. Tasaki rumanah tayi bedroom dinta tanaji ajikinta haqqin rumanah bazai taba barinsuba. Jiki amatuqar sanyaye ta juya ta fice Jakadiya tabita da kallon tausayi. Tana zuwa dakinsu ta zauna bakin katifarta tareda rafka tagumi ta fada tunani. Nuratu ce tashigo dakin tayi saurin isa gurin rumanah din kawai ta rungumeta Tana cewa, Rumanah karki karaya kisake jajircewa kina haquri da mamani zata daina wata rana ko ance tayi bazatayiba. Murmushi mai ciwo tasaki tareda kallon nuratu tace, Mamani uwace banta6a riqeta arainaba. Zuciyarki nada kyau rumanah Allah yabarki ahaka. Murmushi tayi tace, Ummana,abbanah da ammy bayansu kece mutum 'daya dana sani mai zuciya mai kyau Dan haka keda ammy Allah kuma yabarku ahaka. Dariya sukayi suna qoqarin manta damuwar abinda yafaru. Ahankali nuratu takalleta tace, Rumanah kintuna lokacinda muke wasar riqe riqen gudu da ruwa a cup a dakin nan? Murmushi tayi tareda kallon nuratu sbd wannan wasar itace abinda bazata ta6a mantawaba a quriciyarta, Itace abinda nuratu ke tuna mata tasakata nishadi amma yau saitaji jikinta yayi sanyi tace, Meyasa kika tuna wannan yanxu? Haka kawai na tuna sbd bansaniba kobazamu sake samun damar tunawaba irin haka cikin jindadi. Qurawa nuratu ido tayi zatayi magana aka shigo dakin. Kallon qofa sukayi sukaga bayi kusan biyar atsaye saiga Jakadiya tashigo fuskarta a tamke babu alamar wasa takalli rumanah ta 'dauke kai ta juya Tana cewa, Ku taho da ita zuwa part din gyara yanxunan. Tana fada ta fice sbd kar tausayin rumanah yashigeta. Kallon juna sukayi itada nuratu irin kallon da nuratu ke mata na tsananin tausayi yasa tayi saurin kallon qofar da jakadiya ta fita tayi kafin tasake kallon nuratu da tuni hawayen rabuwarsu ya gangaro mata. Matsowa sukayi suka kama hannunta ko qwaqwaran motsi bata iyayi suka fice da ita. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *15* Shiru sultan yayi yana sauraren bayanin Jakadiya ya lumshe idanuwansa ya bude, Allah yataimaki sultan sarkin dayafi sarakunan qarninsa Haryanxu baiwa rumanah bata zama cikakkiyar baiwa ga yarima ba"""""" Sune abinda Jakadiya tafada yasaka kallonta kafin cikin 6ayyanarda ikonsa yace, Asanarwa yarima na sauke zaraah daga yau nabawa adama sultana kuma na dakatarda ita daga matsayinta na matar sultan harsai ranarda ya hada shimfida da baiwar. Wani irin yawu Jakadiya ta hadiye cikeda rawar murya da girmamawa tace, Angama da yardar Allah. Tana fita aka isarda saqon ga yarima. Aje cup 'din hannunsa yayi tareda rintse idanuwansa dasuka canza lokaci 'daya yabudesu yakalli ammynsa dake zaune taredashi a dining din palonta sunacin abinci. Lumshe idanuwa sultana tayi ahankali tareda daukesu daga maheer daya qura mata sbd karya gano halinda tashiga ta miqe ahankali ta nufi hanyar bedroom dinta ya riqo hannunta tareda dawo da ita ya rungume ahankali. Zamewa tayi takallesa tareda sakin murmushin dole cikin kulawa tace, Karka takura kanka kayi abinda bakada ra'ayin so zan iya qarasa rayuwata akan wannan hukuncin nasa matuqar baka cikin takura maheer..... Ahankali yabude baki cikeda kulawa yace, It's okay ammy zanyi abinda yace ba buqatar ki damu da idan inaso ko banaso. Bazaka kallesa ka gano 6acin ransa sbd kyakkyawar fuskarsa koyaushe bata nuna 6acin ransa amma Tsananin 6acin ran dayake ciki ayau yafi na kullum sbd sultan nason ganin iyakarsa koyaushe da mahaifiyarsa yake amfani Dan cimma buqatarsa garesa Dan yasan aduniyarsa babu kamar mahaifiyarsa agurinsa. Yau wani irin sabon turare Jakadiya tasa aka kawo daga gidan turaren dake qasar Wanda yafi kowane turare dadin qamshi da hanawa duk namijin daya shiga hancinsa nutsuwa. Farar rigar bacci yau aka zabo mata daga closet tasaka akaro na farko da aka hanata saka bra jakadiya dakanta ta bita koina da turaren ta feshe kafin suka fito. Kamar koyaushe tana shiga Jakadiya ta juya ta fice daga part din. Ahankali ta nufi gurin kwananta. Hasken blue and red bulb ya gauraye dakin. Cak ta tsaya tsakiyar dakin bugun zuciyarta na canxawa har kirjinta yana dagowa amma takasa juyowa. Akaro na farko daya qurawa wata mace daba matarsaba lazy eyes dinsa, Dogon wandon kayan baccine kawai ajikinsa fari qal mai matuqar santsi da laushi, Wani irin murdadden namijine maji qarfi da kyawun gabbai sbd yawan yin geam ya bude duk wani qarfi na jikinsa. Abayanta taji tsayuwarsa numfashinta ya tsananta fita hannuwanta da qafafunta suka fara rawa ta rintse ido. Bayanta dayake fari qal yaqurawa ido da gashinta daya rufe wuyanta yanaji qamshinta na shigarsa yanason ta6o wani bangaren na sha'awarsa akaro na farko dataji muryarsa cikin wani irin taushi da aji yace, Juyo. Juyowa tayi ahankali tareda sunkuyar dakai tanajin wata irin muzanta na shigarta sbd tanajin kallon dayake bin jikinta dashi na qyama. Kusan atare suka rintse ido suka bude sai acikin idanuwan junansu ta mayarda nata ta rufe da sauri tareda sunkuyar dakai. 'Dauke idonsa yayi tareda juya mata baya. 'Daga qafa tayi duk ilahirin jikinta rawa yakeyi zata wuce yariqo hannunta. Barin jikinta numfashinta ke qoqarin yi tayi saurin Jan boyayyan numfashi yadawo jikinta saidai tuni qafafunta suka kasa riqeta ta zube qasa kan gwiwoyinta tana dafe qirjinta dake bugawa da qarfi haryana mata zafi. Tattara numfashi tayi ta dafa table din dake tsakar dakin ta miqe har lokacin numfashinta bai daina fita da sauriba jikinta bai daina rawaba ta fuskacesa kanta na sunkuye. Sake kafeta yayi akaro na biyu. Hannu ya daga yamatso da ita sosai har kirjinsu na haduwa musamman idan numfashinta ya taso sosai qirjinsu ke haduwa. Ahankali yadauke fararen idanuwansa daga fuskarta zuwa qirjinta dake gugar nasa. Hannu yadaga ya dora akafadunta yana kallon idanuwanta dake rintse hawaye na qoqarin fitowa cikinsu. Ahankali ya zame siririn hannun fingilalliyar rigar dake jikinta data gama bayyana komai na surar jikinta. Zamewa rigar tayi tafadi qasa Rintse idanuwansa yayi tareda ja baya ya juya tareda kallon jikinsa ganin tsikar jikar jikinsa ta tashi abinda baitaba yiba kenan tun tashinsa. Bakin gadonsa ya isa ya zauna tareda zamewa ya kwanta rigingine ya rufe idanuwansa batareda yasake kallon sashen datake ba. Daukar rigarta tayi tamayar jiki amatuqar sanayaye ta matsa inda take rabewa ta lafe hawaye suka gangaro mata ta goge ahankali tareda rufe ido. Har asuba tayi babu Wanda yayi bacci acikinsu tanajin anyi kiran farko ta miqe ta nufi qofa tana fita Jakadiya na isowa taqare mata kallo bataga alamar komaiba tasaki ajiyar zuciya afili kafin tamiqa mata doguwar rigar tasa suka wuce. Yau ko palon farko bai iya fitaba sbd bayason magana ko 'daya yau sultana ma saidai yayi mata massage Fruits 'dinda ke cikin small fridge Din bedroom din kawai ya iyasha Sam yau ko apatite bayada. Yau rashin sukuninta yafi na kullum sbd har dare yasakeyi jikinta bai koma daidaiba ko cup tariqe hannunta rawa yakeyi data duba taga dare yakusa yi sai gabanta yafadi saidai tana bawa kanta hkr da qwarin gwiwa Babu abinda takeson gani yanxu kamar nuratu, Tana tsananin buqatar Wanda zatai magana dashi koda so dayane ayini. Da daddare tun gurin kaita Jakadiya ta lurada yanda take cikin tsananin damuwa tashareta suna isa tashige itakuma tadawo. Zaune yake akan cauch 'din datake lafewa gefen yana aiki da apple laptop, Fararen kayan baccine ajikinsa as usual ya miqe qafarsa akan glass center table dake gaban couch din. Ba haske adakin sosai saidai tana iya ganinsa yana iya ganinta. Tsayawa tayi takasa qarasawa kujerar sbd ganinsa agurin. Aikinsa yakeyi hankali kwance batareda yanuna yasan da alamar wani mutum adakinba bayan kansa., Saida yagama ya ajiye laptop din tareda miqewa ya nufi lafiyayyan royal bed dinsa ya kwanta Kansa na sarawa. Saida yakashe wuta yana kalli ta qarasa ta kwanta qasa ahankali. Gurin datake yaqurawa ido itama ahankali tabude idanuwanta ta qurawa gadonsa ido akaro na farko Duk da akwai duhu adakin. So kusan hudu yana gwada ta6ata kozai iya kwanciya da ita amma Sam zuciyarsa na qyanqyami da hakan Wanda hakan yayi matuqar tunxura sultan yayi wani irin fushi mai muni tareda yanke wani irin mummunan hukunci aransa yace adaren yau idan yarima bai keta budurcin baiwa rumanah ba washe gari su saurari hukuncinsa. Koda saqon yaje masa baidamuba matuqar hukuncin kona menene bazai shafi ammynsaba. Jin sanarwar abinda sultan yafada ya tsananta damuwarta da quncinta saidai batada Wanda ko fira dashi bare Wanda zata tattauna damuwarta dashi shiyasa taqara rungumar qaddararta tana jiran hukuncin yanda za'a cigaba da yanda akaso da ita. ** Sama sama Cikin bacci take jin kukan yara da manya, Mazaje da mata tareda wata irin iska mai daukeda hayaniya na amsa kuwwa ako ina na cikin masarauta da wajenta koina na amsawa a fadin garin. Bude ido tayi ahankali tareda kallon inda take tayi ido biyu da maheer duqe agabanta yana idanuwansa sunyi wani irin mummunan ja wata irin damuwa da tashin hankali tareda neman mafita take hangowa acikin idanuwansa., Da sauri ta sauko daga gadon taji qafafuwanta sun nitsa cikin ruwa ta sauke idanuwanta ta duba a firgice tayi baya jikinta na wata irin rawa ganin jini kwance yana gudana. Kallon maheer tayi da sauri ya girgiza mata kai cikin wata irin murya mai ciwo da sanyi yace, mineelik assultana the redblood Queen. Zaro idanuwa tayi cikin tsananin tashin hankali jin abinda yace, Rawa jikinta yadauka Ihun datake ji tun farko yafara yawa cikin kunnenta yana neman gigitata ta fita da sauri tafara gudu cikin jinin daketa gudu kamar ruwa ako Ina na bangon masarautar stains ne na jini, Tana fitowa babban filin harabar palace din taga gawarwaki harbabu gurin saka qafa su zaka taka dole ka wuce ga ruwan sama dake sauka sosai Wanda suke qarawa jinin dake zube koina gudu. Wata irin busa taji anyi wadda ta amsa kuwwa koina Nan take taga mutane nata taruwa kamar tururuwa sbd mugun yawansu, Haka suka cigaba da taruwa suna kallon wata babbar qofa dake been sama inda sultan ke fitowa idan zai fito yayi magana inda kowa ke iya ganinsa. Kutsawa tafarayi Cikin mutanen tana bin mutanen da kallo Nan tafara girgixa kai ganin ba jama'ar daularsu bace kawai hardana wasu daulolin, Wanda alamu suka nuna da qarfin mulki aka mallakesu ana mulkarsu harsu har sarakunansu. Saida aka taru harbaka iya qwaqwaran motsi sbd taro da yawan jama'a aka sakeyin busa nan guri yayi tsit ko kukan tsunstu babu kowa yamaida kallonsa ga qofarda sultan zai fito itama tayi saurin kallon qofar daidai lokacinda aka wangale qofar wadda tafi kama data zinari sbd kyalli. Cikin wata irin doguwar Riga maroon colour tana ja da qasa tafito daga cikin qofar ta bayyana Gashinta azube yake har bayanta yaji adon sarkokin zinari nakai har zuwa kafadunta hakama wuyanta sarkace har saman cikinta ta zinari, Wani irin kyau da kyalli take fitarwa daidai hannuwanta a lalace suke kaca kaca da jini har jikin rigartama haka kujerar karagar mulkin mineelik Wanda keta tsiyayar jini wasu irin samudawan guards suka ajiye mata tasaki wani irin qayataccen murmushi zata zauna...... Cikin wani matsanancin ihu takira sunanta da qarfi tana cewa, Rumanahhhhhh karki zauna a wannan kujerar......rumanahhhhh Zama tayi cikin wani irin iko da mulki nan gari yadauki ihun sunanta. Amatuqar gigice sultana ta zabura daga baccinta tana tareda lalubar bedside lamp takunna da sauri jikinta na muguwar karkarwa tafara karanta innalillahi tana hada wani mugun gumi., Wannan mafarkin nata babu alkhairi acikinsa, Meya hadata da wannan mummunan mafarkin? Tsoro da fargaba taji yana shigarta tayi saurin saukowa tafada toilet tayo alwala tazo tafara jera nafiloli kafin asuba tayi. Har gari ya waye bata sake ko kwanciyaba bare rintsawa, Abinda tagani amafarki tamkar wani gargadine ga abinda suke shirin yiwa rumanah bata fatar ko acikin bacci tasake irin wannan mafarkin bare ya tabbata. Dan haka ta yanke shawara komai zai faru shirye takeda daukar hukuncin sultan. Qarfe goma sha 'daya na rana saqon kiran sultan yazo gareta babu bata lokaci ta miqe cikin shirinta da adonta ta nufi part dinsa kuyanginta na biyeda ita, Duk inda ta gifta kafin ta qaraso anrabe anxube qasa ana gaidata cikin matuqar girmamawa harta isa tun a qofar palon farko suka dakata itada Jakadiya data fito tarbonta suka qarasa. Tana isa jikinta yayi mugun sanyi sbd ganin yanda kowa ya dauke wuta sai mizurai akeyi sbd ran sultan ya baci kuma kowa yasan hukuncinsa ba sauqi ba kyau haka itama ta isa kujerar dake matsayin tata tazauna bayan ta kwashi gaisuwa. Maheer ransa amatuqar bace yake sbd baisan hukuncinda sultan zai yankeba akan ammynsa. Cikin kakkaisar murya yakalli Jakadiya yace, Inason jin dalili qwaya 'daya daya daga yarima Wanda ya hanasa cika umarnin sultan dinsa. Cikin rawar murya Jakadiya takalli yarima zata maimaita masa abinda sultan ya tambaya batareda yakalli ko dayansuba kai tsaye yace, Banada sha'awar kowace mace bayan wadda igiyoyin aurena suke kanta. Wani numfashin bacin rai sultan yafitar yana kallon yarima sbd yasan daga yau hukuncinda zai yanke akansa yagama da rayuwarsa gaba daya cikin isa da mulki yabude baki yace, Jakadiya atambayesa yana buqatar qarin lokaci kokuwa shikenan...... Cikin tsananin dauriya da danne fargabarta da fargabar abinda zai biyo bayan abinda zatayi tabude baki tace, Ina neman afuwar sultan amma baiwa rumanah ta haramta garesa daga yau sbd na 'yantata daga wannan lokacin harzuwa qarshen rayuwarta, Daga yanxu ita ba baiwa bace sbd haka ta haramta ga kowane namiji idan ba mijin aurentaba. Cikin wani irin mugun mamaki da 6acin rai dabai taba yiba yake kallonta jin abinda tafada, Ta 'yanta baiwarda yabada umarnin yarima ya kwana da ita kenan 'danta takare daga aikata abinda baiso Tabbas zasu 'dandani hukuncin sultan daga ita har 'danta. 'Dagowa yayi yakalli wazirinsa cikin wani irin yanayi na nuna rashin damuwa yace, Ta 'yanta baiwarta sbd ta rahamtata ga 'danta sbd bayaso nikuma zan halasta masa ita ayau sbd umarnin sultan baya bin iska, *_KUJE ABADA SANARWAR 'DAURIN AUREN YARIMA MAHEER IBN ABDULSHAMS ABDALLAH DA 'YANTACCIYAR BAIWA UMMU-RUMANAH BULAMA_* nanda awa biyar duk Wanda baizo ya shaida 'daurin aurenba nakoresa daga qasata sai bayan shekara biyar yadawo.,, *_SULTANA ZAARAH BAYAN 'DAURIN AURE ZATA KOMA GURIN IYAYENTA BAZATA DAWOBA SAI MATAR YARIMA MAHEER RUMANAH TA HAIHU._* #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *14* Gyara tsayuwa suhailat tayi daga bakin tafkeken windon bedroom dinta iska na daga curtains suna ta6o har fuskarta sbd sosai take buqatar iskar sanyin AC bazai mata ba she's feeling suffocated already. Gyara tsayuwarta tayi akaro na ba adadi tana tsananin buqatar Wanda zai bata kulawa ayanxu sbd wani irin kishin mijinta dakecin duk wani jini dake yawo acikin jijiyoyin jikinta, Tana tsananin so da qaunar maheer, Maheer na respecting relationship dinsu sbd 'yaya dakuma zaman fahimta dasukeyi Saidai maheer na buqatar macen dazaiji dadin yin rayuwarda yakesonyi da ita Wanda bata fatar yasamu hakan daga wata macen bayan ita, Yanda labari yazo mata baiwa rumanah ce aka za6a Tsoronta na qaruwa aduk lokacinda ta tuno kamanni da tsarin rumanah din Saidai kuma bata tunanin tafi bata tausayi sbd sanin waye maheer bazai ta6a iya kwana da wata mace ba musamman wadda ba matarsaba. Girgiza kai tayi tana mayarda dogon gashinta daya barbaje baya ta zauna bakin lafiyyan gadonta tana cewa, Ya Allah ka yayamin wannan azabar danakeji cikin raina Hawayen datake dannewa tun lokacinda zancen yazo mata suka 6alle ahankali tafara fitarda sautin kuka tana rufe fuskarta. Kallo daya yayiwa gefenda take ya nufi bedroom yashiga ya tube yashiga cikin bathtub yakwanta tareda rufe ido yana qoqarin samun nutsuwa azuciyarsa har tsawon lokaci kafin yayi wanka yafito 'daureda towel milk colour yanufi closet yadauki kaya yashirya cikin kayan bacci ya fesa turare mai sanyin qamshi ya nufi gadonsa ya kwanta hankali kwance cikin nutsuwa tareda shigewa lallausan duvet ya zira hannu yakashe wuta ya lumshe ido sbd shi baimasan ta yaya zai saka zancen sultan aransaba bare harya cika kwata kwata shi ba mutumne mai yawan maganaba idanuwansa da kallonsa suke bada magana ko umarnin abinda za'ayi kuma shima mutumne dazai iya 6ata lokacinsa gun abinda baima shafesaba kokuma abinda baidauka da mahimmanciba shiyasa ko kallo baiwar bata ishesaba idan sungaji da kawota zasu daina Dan Kansu ko yanxu yabartane aringa kawota sbd abinda sultan yafada akan ammynsa if not baisan yama za'ai yaringa kwana daki daya da wata macenba bayan ko matarsa basa kwana daki daya. Tunda yashigo ta lafe jikin kujerar tareda tsayarda duk wani motsinta ta sunkuyar dakai numfashinta na tsananta fita Tana rabe kanta sunkuye yayi duk abinda yakeyi ya kwanta tana ji tana jiran taji ya tunkarota amma ko kallon inda take baiyiba harya kwanta. Ajiyar zuciya tasauke ahankali hawaye masu sanyi suka gangaro fararen idanuwanta bada damu data sharesuba sbd duhune adakin ta kwantarda kanta kan gwiwoyinta hawayenta nacigaba da gangarowa. Asubar farko Jakadiya tazo ta tsaya palon qarshe riqeda doguwar rigar dazata rufe kayan barcin dake jikinta. Miqewa tsaye tayi jikinta ba qwari sbd kuka da rashin bacci ta nufi qofa. Alarm din gefen gadonsa dake tadashi sallah sbd ba'a shigowa ko palonsa na biyu bare atadashi sallah yasa yakeda alarm na tadashi sallar asuba kawai. Ringing alarm din yasa ya cira hannunsa daqyar cikin bacci ya danna hasken wutar dakin Tayi saurin juyowa afirgice sbd takai tsakiyar dakin takusa isa qofa daidai shikuma ya bude oily eyes dake cikeda bacci suka sauka akanta, Dishi dishi yake ganinta ya lumshe idanun yabudesu itakuma hartayi saurin ficewa. Tana ganin Jakadiya tsaye wani irin tsoro da mamakinta suka kamata amma saita sunkuyar dakai jakadiya ta miqa mata rigar ta sanya tareda janyo hular rigar ta rufe fuskarta suka fice. Kallo daya Jakadiya tayi mata tasan babu abinda yafaru tsakaninsu tasaki numfashi tana cigaba da tafiya. Suna fitowa qofar part din bayinda aka bari da Daren still sunan suka Mara musu baya suka kaita sabon gurinta suka wuce batareda Jakadiya tace da ita qalaba. Zamewa tayi qasa bakin gado ta ta qurawa window ido ta fada dogon tunani fuskarta cikeda damuwarda tayiwa rayuwarta dabaibayi. Tadauki lokaci kafin tamiqe tashiga makeken bathroom din dake dakin tayo alwala ta zame kayan jikinta tareda mayar musu da kayansu cikin wardrobe tasaka doguwar Riga tayi sallah. Koda gari ya waye ankawo mata abinci bata iyacin komaiba hakama da rana ankawo amma takasa koda kallon abincin. Arayuwa yanxu batada wani sauran buri ko mafarki sbd yanxu ta yarda mafarki baya zama gaskia, Ita ayanxu tamkar wata dabbace da duk yanda akaso ayi da ita haka za'ayi ta yarda da qaddara tabarwa Allah alamuranta. Sultana bawani doguwar nutsuwa bace acikin zuciyarta sbd har lokacin zuciyarta da gangar jikinta sunkasa nutsuwa da alamarin tsoro take ciki sosai sbd tana tsoron abinda zai iya juyewa gaba. Koda gari ya waye Jakadiya tasanarda ita babu abinda yafaru tsakaninsu hakanan tasamu kanta da ajiyar zuciyarta tayi shuru tsawon lokaci kafin takalli jakadiya cikin wata irin murya tace, Jakadiya zansa acirewa rumanah mahaifa sbd fargabata tana yawa Wanda hakan nabani cewar zata iya haihuwar namiji Wanda nibana mata fatar zamowa MINEELIK-ASSULTANAH kuma kinfi kowa sanin me hakan ke nufi, Tayi yarinya da riqe wannan matsayin sbd bala'i da masifar dake ciki yafi qarfin shekarunta Dan haka abin zaifi ta6ata. Shiru Jakadiya tayi kafin tagyara zama cikin son gyara zancen tace, Allah yataimaki sultana cire mata mahaifa tamkar mun qarasa nakasta rayuwartane, Ke tamkar uwa kike agareta muyi mata fatar samun 'ya mace ta yanda idan tasamu yantawa akorata nesa da nan taje tayi aure tafara gina wata sabuwar rayuwar. Ajiyar zuciya sultana tasaki tareda lumshe ido tana fatar Allah karya bawa rumanah cikinma kwata kwata ana dakatarda ita daga zuwa gurinsa ta 'yantata ta turata nesa da nan. Mamani duk wani baqin ciki da quncin duniya yataru axuciyarta tun lokacinda aka tafi da rumanah ko ruwa ta kasa sawa cikinta jitakeyi kamar zuciyar naci da wutane saidai tana addua da fatar Allah yasa ko cikin 'ya mace karta samu bare na namiji. Sarauniya adama kuwa komawa tayi tamkar zata mutu sbd baqin ciki acikin dakinta laifi qalilan zakayi tasa arabaka da lafiyarka sbd ta daura damarar yaqi da duk Wanda zaishiga tsakaninta da abinda take buri tun tana qanqanuwarta. Kamar jiya qarfe goma aka zo tafiya da ita bayan anshiryata cikin rigar da gwara ta jiya da ita suka tafi. Yauma a qofar shiga bedroom dinsa ta zame rigar sama da ribbon gashinta ya zubo dakanta yau ta bude tashiga batada kuzari ko kadan ta nufi inda ta ra6e jiya tazauna tareda kwantarda kanta kan gwiwoyinta ta rufe idanuwanta ahankali. Kwance yake duk yau ko ina bai fitaba iyakacinsa palonsa na biyu inda nan yake cin abinci sbd nan ne dining room dinsa, Ko suhailat ma so 'daya takirasa awaya tana qoqarin boye damuwarta da kishinsa tagaidasa tabasa su amah sukayi masa 'Dan surutunsu Wanda duk sukeyin abinsu iyakacinsa sauraransu suka gama. Ammynsa ma yau awaya yagaidata koina bai fitaba yayi kwanciyarsa. Tun lokacinda tashigo yaganta ya rufe idanuwansa ahankali tareda gyara kwanciya sai alokacin ta fahimci yana 'daki sbd duhu bata luraba amma ko motsawa batayiba tayi Shiru ko tunanin bata iyayi yanxu Ahaka asuba tayi ta miqe jikinta amatuqar sake ta fice. Ahankali kwanakin suka ja kusan sati biyu ana kaita amma baitaba ko kallon inda takeba. Abu 'dayane daya fara canzawa shine qamshinta daya kama koina acikin dakinsa har toilet dinsa Wanda hakan ne kesakashi 6acin rai wani lokacin. Itakuma ayanxu tarigada tasan bazai ta6a yin komai da itaba shiyasa kowane irin kaya aka bata bata damuwa sawa takeyi. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *17* Jikinta har rawa yakeyi gurin zuwa tasanarda mamani, Da ace bawa nada ikon gudu Dan karan kansa ba sakasa akayi to yau da bazata tafiyaba gudu zatayi domin ta isa gurin mamani da wuri tafada mata kyakkyawar rayuwarda tayiwa rumanah qwanqwasa. Tana isa babban kicin din ta sake nutsuwa Cikin girmamawa take gaida masu kula da bayin sakewa masarauta girki harta isa gaban mamani dake kwashe farfesun wani qatoton kifi ahankali sbd karya wargaje ahaka ake dorasa cikin inda za'a kaisa, Murya qasa qasa cikin tsananin farin ciki tace, Mamani a yau sultana ta 'yanta ummu-rumanah sbd aurawa yarima maheer ita ataqaicema an 'daura au........ Cak mamani ta kafe idonta akan fuskar nuratu 'din babu alamar motsi atareda ita Cikeda tsoro ta ta6ata tace, Maman........bata qaraba taga ta yanke jiki ta fadi cikin tsananin tsoro da fargaba takira sunanta da qarfi Wanda yasa masu kula dasu qarasowa da sauri suna tambayar abinda yasameta. Girgiza kai nuratu tayi idanuwanta na cikowa da hawaye sai dai batasan mezataceba Dan tasan tsabar hassadace ta sumar da mamani. Ruwa akace nuratu ta 'debo sbd rikicewa ta ciko silver da ruwan masu tsananin zafi tana qarasowa ta zuba matasu amatuqar gigice mamani ta saki wahalalliyar ajiyar zuciya tareda bude ido ta tashi zaune jikinta na wani irin sililin zafi ta 'dago ahankali tana kallon nuratu ta tuno da abinda tafada mata wani irin kuka ne ya kufce mata hadda shesheka ita shikenan rumanah ta mayar mata da burinta mafarki, Ita sai yaushene bulama da iyalinsa zasu bari taringa samun abinda take burin samu, Rumanah tasan duk burinta akan nuratu ne tasamu wannan matsayin amma ta shiga tsakaninta da burinta. Wani sabon kuka tafashe dashi tareda miqewa tana qoqarin cigaba da aikinta sililin jikinma tuni baqin ciki yasa batajinsa ko kadan. Saidai ita mamani kutti ayau tana rantsuwa dasai ta raba rumanah da duk wani farin ciki dazai shigo rayuwarta kamar yanda iyayenta su asma'u suka rabota da farin cikinta, Hakama tayi alqawarin shiga tsananin ummu-rumanah da duk wani burinta kamar yanda ta rabata danata. Jiki amatuqar sanyaye nuratu ta juya tabar sashen kicin din tana tunanin tabbas mamani bazata bari azauna lafiyaba saidai dukda tana mahaifiyarta bazata ta6a bari ta cutatarda ummu-rumanah ba koda hakan na nufin zasu raba hanya ne. Cikin wani irin yanayi yashigo part din na sultana tareda Jakadiya dake biye dashi daukeda sadakin rumanah 'din fuskar yalwace da farin ciki. Suna shigowa dukkanin wainda ke palon suka miqe banda sultana da rumanah dake zaune cikin lullubi. Tsayawa yayi batareda yakalli inda takeba Ganin haka yasa sultana miqewa tsaye tareda riqo rumanah ta tayarda ita ahankali takawota gabansa suna fuskantar juna Tanajin yanda dukkanin jikin rumanah yake rawa haka ta saketa tareda saka hannu ta yaye mata lullubin. Kamar bazai kalli fuskarta ba ya bude fararen oily eyes dinsa akanta, Karo na farko daya kalli wata mace a duniya yaji gabansa yayi mummunan bugawa ya 'dauke idanuwansa ahankali cikin rashin kulawa yayi Jakadiya wani kallo a hanxarce ta matso tareda miqawa ummu-rumanah tray dinda yake daukeda sadakinta cikin tsananin girmamawa tace, Allah yataimaki amarya ummu-rumanah ga sadakinki Allah yayiwa aure albarka. Hannuwanta dake cikeda awarwaro da zobunan zinari ta 'dago yana rawa sosai ta karbi tray din har lokacin kanta na qasa bata dago takalli kowaba. Sultana ta miqawa tray din batareda tace komaiba sbd bazata iya maganaba itadai duk yanda sukazo haka zata bisu sbd tasan wannan shine fate dinta. Karba sultana tayi tareda sakin murmushin qarfin hali tace, Allah yayiwa aure da rayuwaki albarka ummu-rumanah bulama. Mayar mata da lullubinta akayi suka dunguma zuwa gurin sultan . Acikin dubban taro aka gabatarda ummu-rumanah bulama amatsayin sabuwar matar yarima. Jama'ar gari da wasu masarautun sun jinjina kyawu irin na ummu-rumanah sbd ayanda tarihin sarakunansu yake zuwar musu shigowar mace mai tsananin kyawu a cikin zuriar sarauta baya zamtowa alkhairi. Ana gama gabatarwa aka mayarda rumanah gefenta tareda sabbin bayi da kuyangi goma. Bayan angama shagalin sultana ta shirya dukkanin kayanta tareda sa jakadiya tasa ayi mata booking ticket na flight dinda zai tashi da dare zuwa Libya. Wanka yayi yashirya cikin fararen qananan kaya transparent marasa nauyi shiyasa mur'dadden jikinsa yake kusan a bayyane sbd shi Sam bayajin damuwar komai sbd auren bai sakasa akansaba sbd yasan bazai ta6a takura kansa ya canza sbd waniba, baya buqatar wata mace arayuwarsa bayan suhailat so bayajin yanada wani lokacin 6atawa gurin zama yana yiwa mata ciki saikace wani injin. Damuwarsa 'dayace barin sultana masarautar zai ta6a martabarta da qimarta a idanuwan mutanan da mineelik ke mulki dakuma mutanen masarautar mahaifinta. Kwanciya yayi tareda lumshe ido. Suhailat kwananta biyu bata fito part dintaba sbd nauyin ciki dakuma rashin son kusanta kanta da duk inda zataga ummu-rumanah kokuma zancenta sbd batason kishinta yafi qarfinta qarshe tayi abinda zata zubarwa kanta mutumci tabarwa kanta da 'yayanta abin fa'da gashi maheer ma anyi mata iyaka da ganinsa sai baiwarsa tasamu ciki shiyasa ta kama kanta a part dinta tasamu ta haihu ta tattara takoma Georgia ko zata samu hankalinta yadan kwanta. Zaune take a palo tana waya da mum 'dinta cikin sanyin murya tace, Mum inason nazo gida na haihu agurinku sbd nasan anan ne nida abinda zan Haifa zamu samu soyayya da qaunar yanda muke buqata.... Cikin rarrashi mum dinta tace, Suhailat my dear kiyi hkr tunda kinsan a inda kike aure, Idan kin haihu I promise to come by Allah's grace my dear, Kicire damuwa da tunanin komai sbd condition you're in., Wen is your edd??? Saura sati hudu. Ok akwai sauran time ma ashe? Yes mum, Mum can you just give me a minute I will call you back someone is here. Aje wayar tayi tareda kallon Jakadiya data shigo daukeda kaya batai maganaba tagyara zamanta tana jiran jin mai zata fada. Kai tsaye jakadiya tace, Saqon tausar zuciya ne daga sultana na aure da yarima maheer yaqara ayau Allah ya sanyaya zuciyarki. Kasa motsi tayi sai ido data kafe Jakadiya dashi, Wani irin radadi da ciwo ya ziyarci zuciyarta da mararta alokaci 'daya Rintse idanuwanta tayi da sauri hawayen dasuka cikasu suka gangaro tayi saurin dafe mararta tareda fara qoqarin tashi sbd jin danshi nabin qafafunta. Jakadiya ganin halinda tashiga da jinin dake gangarowa daga qafafunta yasa tayi saurin qarasawa gareta daidai lokacinda azaba da ciwon suka taso gadan gadan tasaki wani irin kukan azaba tana dafe cikinta sbd jin axabarda bata taba jiba gurin haihuwa. Ganin abin yayi muni sosai yasa Jakadiya bada umarnin aje atahoda masu karbar haihuwa sbd tanasa ran qila haihuwarce. A gaggauce aka kirawosu suka kamata aka shiga daki da ita nan Jakadiya taje ta sanarda sultana Cikin qanqanin lokaci masarauta ta 'dauka labarin haihuwar da za'ayi saidai kuma masu karbar haihuwar sunkasa sbd jini take fiddawa har lokacin ruwan haihuwarta basu fasheba gashi tafara fita hayyacinta. Cikin gaggawa jakadiya taje tasanarda sultan abinda masu karbar haihuwa sukace na za'a iya rasa ran suhailat da abinda yake cikinta. Jin haka sultan dayace kar asanarda yarima sbd karyaqi tarewa da rumanah yau amma jin za'a iya rasa abinda za'a haifa yasa yace asanarda yarima yayi gaggawar bata taimako sbd bayason arasa abinda ke cikin sbd basusan ko meneneba. Lokacinda ya isa yaga halinda take ciki ransa yayi mummunan 6aci sbd ganin irin jinin data zubar sbd baqin ciki kai tsaye ya fitarda wayarsa yakira khaleefa kai tsaye yace, Khaleefa ina buqatar tickets na jirgin dazai tashi acikin daren yau. Yana kashewa ya matso gefenta ya zauna tareda riqo hannunta ya share mata zufa da handkerchief dinsa cikeda kulawa sbd ganin nata yana qara muni. Fita yayi ya nufi part dinsa ya shirya luggages dinsa ya canza kaya. Cikin qanqanin lokaci aka shiryasu amah. Koda khaleefa yasanarda sultan buqatar maheer Kallonsa sultan yayi yace, Ka karbo musu ticket shida Shida mahaifiyarsa da matansa tareda 'yayansa. Jin haka khaleefa yaje yayi yanda zaiyi ya karbo guda shida 'din koda ya dawo harsun gama shiri tuni jakadiya taje bisaga umarnin sultan ta hadawa ummu-rumanah kaya cikin wasu kyawawan akwatina marasa girma sosai guda uku tasakata ta canza kaya zuwa doguwar Riga baqa suka fito. Sam baisan abinda yake faruwa aka dauki suhailat dake kwance kamar gawa aka saka mota suka nufi airport. Sultana da rumanah taredasu amah kuma suka shiga mota 'daya suka Mara musu baya. Suna isa Sam bai lurada rumanah ba aka dauki suhailat akai cikin jirgi da ita yabi bayansu sultana da yara tareda rumanah da jikinta ke sanyaye suka rufa masa baya. Amatuqar sanyaye take sbd wannan shine karo na farko data taba fitowa daga cikin masarautar tun duk tsawon rayuwarta. Ganin yanayin suhailat dakuma ummu-rumanah yasa sultana yanke shawarar qin zuwa Libya binsu zatayi sbd batasan wani irin riqo su maheer din zasuyiwa rumanah idan basa ganin idon kowa duk da tasan ba ruwan maheer da ganin idon kowa akan alamarinsa. Suna shiga jirgi a darare ta zauna kusada sultana tana kama jikinta kanta a sunkuye har jikin ya daga sama ta rintse idanuwa tareda qanqame jikinta. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *16* Not edited.⚠ Wani irin kallo sultana ta 'dago tayi masa cikeda mamaki da takaicin abinda yake shirin yi kafin ta bude baki tayi magana cikeda nuna isarsa da matsayinsa yace, Lij(sadaukin kuma amintaccen mayaqin meneelik) duk wanda ya nuna rashin gamsuwa da hukuncin sultan ko a fuskane ko wanene shi arabasa da abinda yafiso ajikinsa, Idan nace ko wanene ina nufin kowanene, Jakadiya kije ashirya sabuwar surukar sultan nanbada jimawaba zata zama uwar magajin meneelik. Yana gama fada ya miqe yashige palonsa na hutawa tareda manyan masarauta dazasu tattauna wani abin, Wasu majiya qarfin samudawa suka tsaya qofar Dan bata tsaro. Kai tsaye ya miqe yabar palon batareda fuskarsa ta nuna meke cikin zuciyarsaba. Sultana ma miqewa tayi jikinta amatuqar sanyaye zuciyarta cikeda takaici da tunanin rashin ganin amfanin 'yantawarda tayiwa rumanah tunda hakan baisa ta tsirar da ita daga masifar datake gudar mataba ta haihuwar namiji a wannan masarauta ta mineelik. Jakadiya kuwa wani irin zufa take yarfewa Tana qoqarin ganin ancika umarnin sultan saidai itama damuwarta da tsoronta yahana farincikinta wanxuwa musamman idan taduba yanayin tsoro da fargabar dake yawan samunsu idan sukayi tunanin rabon dazai shiga tsananin yarima da rumanah., Wannan masarauta batada tarihi mai kyau, Jinin mutanen da ake kashewa yananan yana bibiyar duk wani hakkinsa, Masiface acikeda masarautar wadda babu Wanda yasanta saisu dasuka ginu acikinta Har abada bazata ta6a yiwa rumanah fatar shiga cikin jerin wainda masifar zata cigaba da shigarsuba aqarshe tabasu qarshe mai matuqar tausayi da kokawa saidai tasan bawa baya wuce qaddararsa, Duk dubararsu da qoqarin kubutarda ita idan Allah yace tana cikin masu wannan mummunan qaddarar saita shiga. Zubewa sultana tayi kan daya daga cikin kujerun palonta na farko sbd bazata iya qarasawa na biyunba tareda 'dagawa kuyanginta hannu nan suka watse cikin girmamawa. Dafe goshinta dake daukeda adon sarqar zinari tayi tareda rufe ido tarasa wane irin hali zuciyarta take ciki sbd takasa riqe tunani ''daya dazatayi cikin biyu auren maheer da rumanah kokuwa korarda sultan yamata gefe 'daya kuma tsoro ne fal yafi cika mata zuciya. Ya Allah kadubi maraicin rumanah kazaba mata kyakkyawar rayuwa agaba. Tana cikin wannan halin Jakadiya tashigo 'yan mata biyar na bayanta 'daukeda manyan trays suna qyalli kamar zinari suka jeru sanku sunkuye. Kallo daya Jakadiya tayiwa sultana 'din tasan tana cikin tension murya asanyaye tace, Allah taimaki sultana anshirya zuwa gurin shirya sabuwar amaryar yarima maheer sa albarki akazo karba. 'Dago fuskarta datai ja tayi takalli jakadiya batareda tace komaiba ta miqe tashiga bedroom dinta tafito da wani madaidaicin akwati yana kyalli. Zama tayi tareda aje akwatin batareda takalli jakadiya ba murya ba kuzari tace, Allah yasawa aure albarka. Amin jakadiya tace tareda kai hannu tabude akwatin. Sarqoqin zinari ne masu nauyi da marasa nauyi nakai dana qafafu taredana wuya da awarwaro har kusan basa qirguwa. Hannu Jakadiya tasa tana zarosu tana zubawa acikin tray dinda suka shigo dasu harsaida tray din yacika suka fice, Sashen adama suka isa tana zaune cikin royal kushins din dasuka qayata palonta cikeda girmamawa aka iso mata da saqon zuwansu Jakadiya tace sushigo. 'Yan matanda ke bayan Jakadiya 'daukeda manyan trays din takalla cikeda mamaki sbd alamu na sakawa aure albarka zaka bayar., Wane zaiyi aure kuma ayau batareda tasaniba? Lallai ana wasa da ita amma karsu damu da zarar ta 'Dora mazaunanta akan kujerar mulkin mineelik tayi alqawarin bawa dabbobin dake zagaye da qasar naman wainda suke wasa da alamarinta. Cikin girmamawa Jakadiya ta katseta da cewa, Sultana zaarah ta 'yanta baiwarta ummu-rumanah ayau kuma ayau sultan zai aurawa yarima maheer ita akan sadaki tiren zinari, Sultana ta bada nata tiren saka albarkar aure saurake gimbiya adama ina fatar ba'a shiga cikin lokacin hutawarkiba. Cikin wani irin yanayi na mamaki ta kalli Jakadiya tace, Aure tsakanin yarima da baiwa? Kozansan dalilin wannan auren na gaggawa? Allah yataimakeki maganar dai 'dayace. Rintse ido tayi tareda Jan numfashi cikin takaici Sam sultan bazai bari tashaqi numfashi mai dadi ba sbd wannan masifar tasa tason haihuwar magajin mineelik, Meyasa koyaushe yake son 6ata mata aiki idan yayi nisa, Tana qyalewane ta lafe sbd bokanta yace mata sa'arta ba yanxu takeba saizuwa gaba takwantarda hankali tajira sbd ba'a taba haihuwar namiji ba a masarautar yayi duba yaga tabbas mace ce zatayi mulkin mineelik bayan sultan takuma tabbatarda itace macenda zatayi mulki amma badan hakaba da tuni tasaka anbinne sultan da ransa takaiga cikar burinta. Murmushi tasaki tana 'dauke gira 'daya tace, Allah yayiwa aure albarka. Sarkar jikinta data kanta taredata qafafunta tasa baiwarta nuratu ta cire ta daura akan tray din suka miqe suka fice. Nuratu duk ilahirin jikinta rawa yakeyi gurin cire mata sbd tsananin farin cikin data shiga jin zancen, Ta matsu tagama yiwa sarauniya adama yankan fruits taje tafadawa mamani sbd yau tun safe adama tasakata aikin abinci kusan kala biyar sbd 'yarta meenah zata zo hutun makaranta daga Sydney. Part dinsa ya isa cikin wani irin yanayi da babu mai iya gano maike zuciyarsa ya zauna kan sofa tareda rintse idanuwansa yana shafo sumar kansa., Miqewa yasakeyi ya nufi bathroom yashiga cikin bathtub bai tsaya bata lokaciba yayi wanka yafito ya zauna gaban mirror yana goge jikinsa, Shiri yayi cikin Ethiopian royal kaftans black and golden wainda yasaka ranar daurin aurensa da suhailat., Turare yafesa tareda saka takalmi ya fesa turare tareda gyara gashinsa mai 'Dan tsawo ya 'daure tsakiyar kai yasaka hula batareda yakalli kansa a madubi ba ya nufi qofa ya fita inda guards kusan guda goma da fadawan sultan suke jiransa Dan masa rakiya har gurin daurin auren. Zaune take kan kujerar mirror ita kadai kamar koyaushe shiru tayi nisa cikin tunani tareda qurawa kanta ido. Qura mata ido Jakadiya tayi kafin tayi gyaran murya tareda yiwa 'yan matan alama da ido cikin nutsuwa suka zo gaban rumanah data miqe cikeda ladabi tana gaida Jakadiya suka Jere matansu. Sam bata shiga ko saka kanta ga duk abinda tasan bai shafetaba shiyasa ko inda aka ajiye kayan bata kallaba ta sunkuyar dakanta tana jiran umarni daga jakadiya sbd tasan dole akwai abinda yakawota. Fuskarta Jakadiya take kallo tace, Ayau sultana zaarah matar sultan abdulshams sarkin masarautar mineelik ta 'yantaki ummu-rumanah bulama sbd ki auri 'danta 'yarima maheer Wanda za'a daura miki aure dashi yanxu nanda mintuna qalilan. Kallon Jakadiya tayi da kyau taga fuskarta babu wasa ko raini yasa tayi qasa da kanta sbd tasan babu abinda zaisa Jakadiya tafadi abinda bahakaba sbd dokace a masarautar duk Wanda yayi kuskuren qarya aka ganosa allurar dabazai qara maganaba ake masa shikenan yazama kurma shiyasa duk tsanani duk wuya ba'a qarya a mineelik. Shiru kawai tayi sbd haryanxu batajin kanta amatsayi na an 'yantata tunda za'ayi auren manufa da ita, Aurenda tasan dalilinsa Dan haka babu abin murna a 'yancinta. Riqota sukayi zuwa toilet batai musuba jiki asake tabisu. Wani irin gyara na musamman aka hau yimata idanuwanta arufe har aka gama suka fito nan aka zaunar da ita gaban madubi nan wasu mata suka shigo su hudu cikin wani irin ado irin na al'adarsu suka fara gyara mata fuska cikin qanqanin lokaci suka tsara wata irin kyakkyawar kwalliya a fuskarta, Ana gamawa kallo 'daya Jakadiya tayi mata taji numfashinta ya sarqe tayi saurin sakin tari tana dafe qirjinta. Wata irin doguwar Riga fara qal mai adon wasu irin golden stones masu matuqar kyau da qyalli aka saka mata tareda daure dogon gashinta tsakiyar kanta kafin aka saka mata wata irin kyakkyawar doguwar sarqar zinari tareda awarwaronta sai wata irin kyakkyawar sarqar kai data qafafu kafin aka lullubeta da dogon mayafin daya fito daga hannun sultana. Suna gamawa Jakadiya tayi gyaran murya nan dukkaninsu suka miqe tareda miqarda rumanah data zauna sai yanda akayi da ita itadai tasan da dah da yanxu duk 'dayane babu wani banbanci arayuwarta. Kai tsaye part din sultana aka nufa da ita inda ana gama 'daurin aure itace zata kaita ga sultan yasawa aure albarka. Kamar yanda sultan yabada umarni bayan awanni biyar cif dubban jama'ar qasar da maqwaftanta sun shaida 'daurin auren yarima maheer abdulshams da ummu-rumanah bulama akan sadaki silallan zinari guda hamsin. Ana gama daurawa yarima sultan yafara kallo cikin wani irin yanayi na murmushi. Yarima har lokacin baiyi magana ko daya da kowaba har aka watse. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *19* Cikin nutuwarta ta tura qofar palon tashiga da siririyar sallama taga baya palon ta sake hadiye wani yawun tana qoqarin daidaita numfashinta da nutsuwarta ta nufi qofar bedroom din data gani tayi knocking ahankali sbd sanin bayason hayaniya. Jin shiru yasa tasake knocking din amma shiru ganin kar abincin ya huce tayi laifi kuma ga tunanin bayason yin mgn ne yasa ta murda cikin tsoro tsoro ta shiga tareda rufe qofar ta juyo ta tsaya jiran umarni kanta asunkuye yake jin shiru yasata dagowa taga baya dakin saitayi tunanin qila yana dayan dakin harzata juya sai qofar bathroom ta bude ya fito daure da towel a qugunsa light brown sabo qal murdadden jikinsa da muscles sai glowing yakeyi ruwan wanka na gangara alamar tsantsin fatarsa, a tsorace ta kalli qofar idanuwanta yashiga cikin nasa da sauri ta juya masa baya duk ilahirin jikinta da muryarta na rawa tace, Yi,,,ha...kuri ammy tace na.. Tray din hannunta ne ya kufce sbd rawar da jikinta keyi tayi saurin riqewa tana qoqarin saita nutsuwarta sbd jin baice komaiba har lokacin. Bayanta ya qurawa ido duk da tajuya baya yana iya ganin yanda numfashinta ke fita da qarfi sbd kafadunta dake sama suna sauka baisan da ita akazoba saidai kuma baiyi mamakin ganintaba sbd sanin waye ammynsa idan tanason mutum. Closet dinsa ya nufa yaciro kaya marasa nauyi, Wata black transparent Louis vuitton longsleev yasaka da farin wando na Louis Vuitton sai turarensa na Clive Christian imperial Majesty. Duk abinda yakeyi ko ajikinsa baburuwansa da tsayuwarta Zama palo ya nufo batareda yace mata qalaba ganin harya fice baice mata komaiba ta biyo bayansa, A palon ta tarardashi yazauna yana kunna wayoyinsa daya kashe Sanin yanda jinin sarauta yake yasa ta matso gabansa a natse ta ajiye tray din kan table din gabansa ta bude masa komai cikin tsoro tsoro sbd gudun laifi. Fridge ta bude ta dauko ruwa marasa sanyi sosai tazo ta ajiye masa. Kallonta yayi wannan karon ba 'Dan mamaki sbd wannan shine karo na farko dazaici abinci agidansa da ruwa ajiye gabansa tun baici abincinba batareda yace akawo masaba, Koyaushe idan zaici abinci suhailat da mai aikinta Carolina basa kawo masa ruwa kullum saiyace akawo masa bayan yayi nisa dacin abincin. Ficewa tayi tasauko ta nufi kicin suka cigaba da aikinsu. Bayan mintuna Carolina takoma takwaso kayan. Saukowa yayi su amah dake fitowa daga dakinsu suna ganinsa suka zo gurinsa da gudu suna kiran sunansa. Daukar fammah yayi yariqo hannun amah yana cewa, Heyy daddy's girls. Zama yayi kusada sultana yana ajiye fammah kusadashi yace, Gud morning ammy? Morning or afternoon maheer look at the time. Bai kalli agogonba yace, Nace ina kwana ne ammy sbd bamu haduba tun safiyar yau sai yanxu so..... Murmushi tasaki tareda dafa hannunsa dake kan nata ta juyo da kyau takallesa cikin kulawa tace, Yaya suhailat I hope kunsamu shawo kan matsalar? Shafa kan amah yayi yace, Amah take your sister and go to your room idan nagama mgn da ammy zanzo okkk?. Tashi sukayi riqeda hannun juna suka nufi room dinsu da gudu cikin wasa. Lumshe oily eyes dinsa yayi batareda yajuyo yakalli ammyn ba yace, Anmata cs babyn bezo da raiba Sbd wahalar datasha sosai bamason ta farko yanxu saitayi 48 hours. Kallonsa sultana tasakeyi cikin tausayawa tace, Allah yabata lafiya yakuma tsare gaba amma babyn mace ce ko.... Kasa qarasawa tayi sbd faduwar da gabanta yayi na rashin wace amsa zai bata. Its a boy. Kallonsa tayi amatuqar firgice da tsananin mamaki saidai tayi saurin yin istighfar sbd agurin Allah komai mai yiyuwane. Shiru tayi zuciyarta na wasi wasin abinda takeda niyar yi akan zaman rumanah dashi saidai tsoro yafara shigarta, Idan dama 'yaya mata Allah yaqaddaro maheer zai fara haifa kafin yaya maza idan ta tura rumanah gurinsa tasamu ciki yanxu yaya kenan.. Rufe ido tayi Cikin Cikin zuciyarta tace, Ya Allah kasa 'Dan nan daya shi maheer zai Haifa harsai sunsamu makarin dazai karye abinda ke bibiyar sarakunan mineelik. Fitowar rumanah daga kicin zatazo tambayar ko ammyn nason wani tana ganinsa ta juya tun bata qarasoba sultana tabita da kallo tana cewa,Allah yakaremin ke 'yar amanata. Tashi yayi yanufi dakin yaransa ya tararda suna drawings ya zauna bakin pink gadon amah yayi crossing legs ya qura musu ido sun saba da dadynsu bamaison magana bane yasa basu damuba presence dinsa kawai nasasu farin ciki. Saida maraice yaje asibiti ya dudduba reports din suhailat sai bayan magrib yadawo lokacin ammy na bedroom dinta. Kai tsaye ya wuce sama wanka yafarayi yasako jallabiya fara qal tareda tareda sakin gashinsa dakeda 'Dan tsawo ya sauko ya nufi gurin ammy. Yana bude dakin tana budewa ta fito harsaida qirjinsu ya hadu da juna tayi saurin ja da baya tana sauke kai Shikuwa yi yayi kamar baisan meya faruba ya shigo tayi saurin ficewa. Dakinta taje tana shiga ta tube tafada wanka. Tana fitowa tayi sallar ishai ta fesa spray ta saka kayan bacci Riga da wando farare masu santsi tana cikin daure gashinta Carolina tashigo tace sultana nakiranta. Aje daurin gashin tayi ta dauki diguwar riga bai budadden gaba tasa tareda rufe kanta da hular rigar ta fita. Zaune ta tararda ammyn bakin gado cikin shirin bacci cikeda girmamawa tace, Ammy gani. Yauwa rumanah idan kingama shirin bacci kije sama dakin maheer ki kwana can idan zaki kitafi masa da tuffa. To tace kanta asunkuye tareda juyawa ta fice.. Wannan halin na biyayyar rumanah akan kome akasata yasa take qara qaunarta. Bata koma dakiba kicin taje ta bude fridge ta dauko apples din guda biyar ta jera a glass bowl da 'yar qaramar wuqa ta fito ta nufi saman. Sanin qila baya palo yasa ta bude qofar palon ta shiga ta nufi bedroom dinsa tayi knocking ahankali. Saidatayi so uku taji shiru tasan bazai amsaba yasa ta bude dakin tashiga. Zaune yake yana waya da doctor Edward daya kirasa yana fada masa wasu results din suhailat dasuka fito. Gabansa ta isa ta aje kan table din daya Dora qafafunsa ta juya Palo taje ta dauko masa ruwa da cup tadawo ta ajiye daidai lokacin ya gama waya ya miqa mata hannu tabasa ruwan yakarba yasha Kamar bazaiyi magana ba yace bana buqatar apples din yanxu take them back. Dauka tayi tamayar fridge din palonsa tadawo ta dauke cup da ruwan dayasha tamayar saita kasa dawowa cikin dakin ta tsaya qofar dakin tana zullumin komawa kuma bazataso taqi bin umarnin sultana ba koda kuwa a mafarkintane. Tun tana tsaye qofar bedroom din hardai ta zauna bakin qofar dakin ta jingina da qofar ta lufe idanuwanta tana tunanin rayuwarta yanda ta jujjuyawa yau wannan gobe wancen, Tafaro amatsayin 'yar bayi, Tadawo baiwa daga baiwa takoma tamkar sa 'daka yanxu kuma gata a 'yantatta kuma matar 'Dan sarki batasan kuma gobenta meta tanadar mataba. Da asuba ya tashi yayi alwala yasaka jallabiya da farar qaramar hula yasa ya nufi qofa Dan zuwa masallacin da dake kusa dasu na wani balaraben qasar. Yana bude qofa yayi tuntube da ita kafin yayi qoqarin hana kansa kaiwa qasa tuni ya fada samanta da sauri suka kalli juna cikeda mamaki yake kallon idanuwanta dake cike taf da tsoro. Kallonta yakeyi batareda yadagataba kokuma yayi mgn. Idanuwansa yamaida kan qirjinsu dake hade numfashinta dake fita da qarfi yana qara hade jirjinsu. Hawayen azabarda hannunta keyine suka gangaro mata kuma bazata iya cewa yadagaba. Hawayen yabi da kallo kafin yakalli cikin idonta cikin wata irin murya yace, Inada nauyine? Rufe ido tayi ahankali tareda girgiza kai. Sake kallon idonta yayi yagano wani Abu yatashi ahankali ya miqe tsaye. Tashi tayi ta dafa zata miqe takasa sbd azaba Dan taji lokacinda kashin hannunta ya targade. Hannun yakalla nantake yagane taji ciwone yagane dalilin kukanta kenan. Hannu ya miqa mata cikeda bin umarni ta kama ya miqar da ita ta juya da sauri zata fice ya riqo hannun tareda dawo da ita harsaida ta fado jikinsa hular kanta ta Zame. Juyo da ita yayi suna fuskantar juna ya zuba mata idanuwansa tareda kamo hannun ya matsa still idanuwansa na kanta Rintse ido tayi da qarfi sbd zafi cikin lazy voice yace, Akwai zafi? Saki jikinta yayi daqyar ta iya girgiza kai. Mamaki tabasa wani malalacin murmushi ya fito gefen bakinsa ya sake matse hannun sosai sai kawai ganin yayi ta zube jikinsa idanuwanta na rufewa. Shiru yayi yaji tabbas suman azaba tayi ya dago fuskarta yakalleta cikin maqoshinsa yace, Unbelievable. 'Daukarta yayi ya kwantar a kujerar palon ya tayarda sallarsa hankali kwance saida yagama tukuna yadauko ruwa a fridge yazuba mata kadan Ajiyar zuciya tasaki tareda bude idanuwanta ahankali Kan fuskarsa idanuwanta suka sauka ta lumshe ido tasake budewa sai kawai hawaye suka fara gangaro mata. Qura mata ido yayi yana mamakin hawayenta sbd dukkanin alama na ciwon datajine abinda baitaba ganiba ga suhailat duk kuwa wuya da azaba yanada wuya suhailat tayi hawaye Ita kuma wannan hawayen nata na shagwabane tunda daga Dan wannan ciwon sai hawaye. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *18* Tun acikin jirgi aka fara bata taimakon gaggawa jinin ya tsaya amma Sam bata farfadoba koba'a fada masaba mmatsayinsa na likiti yasan ba lallaine abinda ke cikinta ya rayuba musamman dasuka duba cikin ya daina motsi, Adduarsa da damuwarsa itace suhailat ta tsira koda za'a rasa babyn ne. Su amah dake taredasu sultana tuni sukai bacci Sultana takalli rumanah da har lokacin bata iya gano yanayinda ta kar6i aurenta da maheer, farin cik kokuwa sabanin hakan saidai Sam yanayin sanyi na rumanar yakasa saka tagane yanayinta. Cikin kulawa da sanyin murya takira sunanta. 'Dagowa tayi takalleta tareda amsawa cikin sanyin murya kafin ta sunkuyar dakai. Rumanah karki sakawa ranki sbd maraicinki da zamtowarki baiwa duk wannan abin yake faruwa dake Jarabawar ubangiji ce dakuma qaddararsa Wanda tuni ya qaddaro miki hakan, Na tabbarda Allah zai haskaka rayuwarki sbd kinrugumi qaddararsa da dangana., Ina taredake rumanah,ke amanace agurina bazan taba bari ki cutatuba matuqar inada zarafi da ikon hanawa, Naso kubutar dake daga wannan rayuwar ta hanyar 'yantaki sbd ki haramta ga yarima saidai bansan hakan zai qarasa hargitsa komaiba sai kuma Allah yayi yanda yakeso bamuda wani ikon hanawa saidai rumanah qaunar danake miki bazata sa nayi sonkai a wannan al'amariba Yanxu ke ba baiwace kinada iko da ra'ayin kanki matuqar bakya son wannan auren nayi miki alqawarin zansaka maheer yasakeke zan mayardake masarautar iyayena ki rayu cikin aminci da kwanciyar hankali. 'Dagowa tayi takalli sultana Duk wannan alamarin hawaye ko 'daya bai taho mataba sbd tariga ta rumgumi kome yazo da Wanda zaizo amma yanxu wasu irin hawayene suka ciko fararen idanuwanta takalli sultana ta sunkuyar dakai tareda rintse idanuwanta cikin sanyin murya tace, Ta yaya zan bude bakina agabanki ammy nace banason zama acikin zuriarki, Har abada ammy kece mai zartarda hukunci akaina nabisa koda 'yanci koba 'yanci bazan cewa aa ga duk hukuncinda zai fito daga bakinkiba, Ni baiwace sai yanda akayi dani haryanxu ni baiwace agurinki banida zabi sai Wanda kuka zabarmin. Lumshe ido sultana tayi cikeda tausayin rumanah batason takurata amma zasu bawa wannan auren dama basusan abinda Allah ya tanada acikinsaba. Shiru suka sakeyi kowa da tunanin dayakeyi aransa. Qarfe hudu na asuba suka isa, Gida aka wuce da sultana da rumanah tareda yara shikuma maheer tuni motar asibinsa tazo sukai asibiti cikin gaggawa sbd yasan ma dole cs zasuyi mata. Suna isa gidan sultana ta fito motar da kanta tasaka password na securityn gate 'din gidan sbd tasani. Shiga sukai driver yayi parking suka fita yashigar musu da luggage dinsu har first palon dake qasa kafin ya aje keys din motar ya wuce dama drivern dake kaisu amah school ne. Da gudu su amah suka nufi bedroom dinsu bayan Mac driver yakira Carolina a waya yace sundawo tadawo itama tace gatanan zuwa shiyasa suke murna sbd sunason Carolina tana kula dasu sosai. Lafiyayyan babban bedroom din dake gefen nasu amah sultana tace rumanah ta shiga kafin itama ta wuce Wanda yazamto kamar nata idan tazo. Jan kayan sultana tayi tabita dasu tashigar mata har dakin ta ta ajesu kafin tafara qoqarin gyaran dakin sultana ta dakatarda ita da cewa, Rumanah kibarshi kiyi sallah tukuna. Ba musu tace to tareda ficewa taje dakinta Kasancewar batada kwadayin babbar rayuwa yasa duk tsaruwa da haduwar dakin bata tsaya wani kalle kalleba ta shiga bathroom tayo alwala tana fitowa ta bude akwatinda takesaka ran zata samu abin sallah tasamo doguwar Riga da gyalanta ta nada ta fito taje dakin sultana taga inda take kallo tana sallah takoma ta tayarda sallah. Bayan tagama ta cire rigar sallar ta zauna shiru tana qara bawa sultana lokaci kafin ta miqe takoma 'dakinta tayi knocking ahankali kafin tabude tashiga cikin ladabi da girmamawa tace, Ammy barka da safiya. Kai kawai ta daga mata sbd gajiyar da rashin bacci dake tareda ita amma bata iya kwantawa matuqar ba gyara mata dakin akayiba aka canza bedsheets sbd ankwana biyu ba'a cikinsa duk da komai nanan lafiya klau ba'a cewama babu mutane acikinsa sbd babu ta inda iska zaishigo bare yayi qura. Zanin gadon tafara yayewa daidai shigawar Carolina dakin nan ammy takalleta cikin turanci tace takawowa rumanah new bedsheets. Da sauri ta karbi na hannunta data cire taje takawo wani fari qal sbd kusan gidan basu cika amfani da kowane kalar bedsheets ba kamar fari. Karba tayi ta shimfida tafara gyaran dakin sbd Carolina taso karba tace tabarsa ita kanta sultana tafison aikin rumanah sbd itace kawai ke mata aiki yayi mata yanda takeso. Tsaf tagyara dakin ta wanke toilet ta kunna AC da burner nan take dakin ya canza ta fice. Tana fitowa taga Carolina nata aikin gyara koina an kunna duka ac ac da fridge fridge ta bude store ta debo ruwa da drinks ta jera ako wane frudge harna sama inda dakunansu maheer da suhailat suke tuni gidan ya dauki sanyi da qamshi masu dadi Itadai dakinta tashiga tayi wanka tasaka doguwar Riga baqa ta dawo ta zauna bakin gado tana jiran sultana takirata asata aiki sbd ita tafi sabawa da aikin wahalar Sam zama guri daya ko Hutu bata saba dashiba. Sultana bayan takira maheer bata shiga itadasu amah bacci suka kwantayi cikin nutsuwa sbd agajiye suke sunsaba da Hutu su Sam jikinsu bayason gajiya. A asibiti duk yanda sukaso ganin ta haihu da kanta abin ya gagara sbd taqi farfadowa duk wata allura sun mata har naquda suka qwaqwalo mata ta hanyar fasa mata ruwan haihuwa amma shiru shiyasa suka shiga emergency theater da ita kai tsaye sbd suna gap da rasata Dan tuni suka gano babyn ya dade da mutuwa. Bashine yayi mata cs din ba doctor Edward yayi mata shiyasa haryasamu damar zuwa office dinsa yayi amfani da wayar office dinsa yakira sultana yasanarda ita halinda ake cikin. Zama yayi tareda jingina bayansa jikin kujerar ya lumshe idanuwansa Kwanakin nan he is in so much stress daga wannan sai wannan kansa har Sarawa yakeyi sbd baisaba da irin wainnan damuwarba. Cikin ikon Allah anyi komai lafiya aka kaita dakin hutawa Dan har lokacin bata farfadoba, Lokacinda duba gawar babyn saida yaji mumman faduwar gaba tareda dafe goshi kafin yasaki boyayyar ajiyar zuciya sbd ganin namiji ne, Yana son duk abinda matarsa zata Haifa masa sbd jininsa ne saidai bazaiso ta haifi namiji ba yanxu sbd bazai iya bari uwar 'yayansa ta fada cikin harkar sarautar mineelik ba shiyasa ya godewa Allah Dan shikadai ne yasan meyasa yayi hakan. Saidayaga komai yadaidaita jiran farfadowar suhailat kawai akeyi ya nufo gida. Driver yakira yazo yadaukesa. Yana isowa babu kowa a palon qasa sai Carolina dake aikin girka abinci a kitchen yawuce sama kai tsaye. Komai Carolina tagyara a saman tundaga bedroom dinsa harna suhailat da palonsu. Tubewa yayi ya shige bathroom ya shiga bathtub dinda tuni Carolina ta hada masa ruwan wanka cikinsa masu zafi kasancewar ya dade baidawoba yasa suka zama masu 'dumi. Lumshe ido yayi sbd jin nutsuwa tafara jikarsa. Ya jima kafin yayo wanka yafito ya shirya cikin kayan bacci masu laushi ya kwanta cikin gadonsa dake daukeda pillows masu laushi kusan guda takwas tareda shigewa duvet ya lumshe lazy eyes dinsa. Sai qarfe goma sha 'daya su ammy suka tashi nan kowa yayi wanka yafito palo breakfast. Batareda sultana ta kalli Carolina tace taje takira rumanah. Knocking qofar tayi kafin tashiga. Kwance take amma ba bacci takeyiba tana ganin Carolina ta tashi zaune tana jiran jin mezata fada. Sanarda ita tayi ana kiranta ta juya ta fita. Saukowa tayi gadon ta gyara hular doguwar rigarta data zame sbd gashinta da baya daure ga tsancinsa ta nufi qofar ta fita. A palon ta tararda sultana zaune cikin doguwar rigarta mai tsada kamar koyaushe saidai duka sarqoqin kai dana wuya na sarauta datake sawa ko yaushe acan nan babu ko daya ajikinta saidai sarqoqin qafarta da bata rabuwa dasu. Sosai tayi kyau cikin simple shigar shiyasa rumanah tasaki fuskarta da wani qayataccen murmushi ganin kamar hankalin sultana din ya kwanta ta qaraso gabanta tareda durqusawa cikin girmamawa tace, Barka da tashi ammy. Itama murmushi tayi cikin sakewa tace, Rumanah abinci zamuci nace kifito kuma kisaki jiki nan gidan mijinki ne su amah yanxu tamkar 'yaya suke agareki saiki ringa kula dasu kema. Girgixa kai kawai tayi kafin ta miqe ta nufi Carolina dake jera abinci a dining room tana zuwa ta sakar mata murmushi tareda karbar mata tray din samosas dake hannunta itakuma ta dauko sauran kayan suka nufi dining suka aje kafin taje tasanarda ammy angama komai. Saidatayi serving ammy da duk abinda tasan tana breakfast dashi sbd ko acan itace tasan komai na abincin ammy. Su amah kuwa Carolina ce tasan me sukeso ita tayi serving dinsu fammah ma abaki Carolina din ta tsaya tana bata sbd tasaba mum dinta ke feeding dinta idan tanan. Harzata juya ammy tasata dawowa ta zauna a takure sbd rashin sabo acan tasaba layi sukebi abasu abinci suje susamu guri su zauna suci. Cikin tsananin sanyi take cin abincin ammy na lureda ita takyaleta sbd tasan zata saba ahankali. Itace tafara miqewa ta nufi hanyar kicin Dan taya Carolina gyaran kicin din dakuma girkin lunch. Bayan su sultana sungama ita takwashe komai tagyara gurin sbd itadai idanma batayi aikiba batajin dadin jikinta. Sultana palo tazauna kallon wani Arabic progm yayinda su amah sukai dakinsu Dan kallon cartoon. Bata gane maganar Carolina itama bata gane tata amma suna kwatanta ganewa ahaka suka fara aiki suna qoqarin sabawa da juna. Sai qarfe 'daya da rabi yatashi daga barci Ya bude idanuwansa dake cikeda bacci ya kalli agogon gefen gadonsa yaga time ya lumshe ido ya tashi zaune ya sauko gadon ya nufi toilet yayi brush yayo alwala yafito yayi sallah azahar yana gamawa ya tube harzai shiga wanka yadawo yayi amfani da wayar bedroom din yakira wayar palon qasa Carolina dake kicin ta nunawa rumanah dake yanka fruits pancake dindata zuba ta fita da sauri. Tana zuwa ta dauki wayar cikin girmamawa tace, OK sir"""bayan tagama sauraran abinda yafada. Aje wayar tayi harta juya sultana ta tambayeta abinda yace ta fada mata cewa yayi akai masa breakfast dinsa sama maida kallonta ga TV tayi tace takirawo mata rumanah. Tana zuwa tace, Ammy gani. Rumanah ki hada breakfast a tray kikaiwa maheer sama. Yawu ta hadiye ahankali tareda gyada kai ta wuce Dan hadawa. Sanyi jikinta yayi amma ammy tafi qarfin komai agurinta, Shirya komai tayi a tray mai kyau ta fito palon ammy ta nuna mata hanyar zuwa sama ta juya jikinta nafara rawa tana qoqarin saita kanta. Harta fara hawa sultana tace, Rumanahh. Cak ta tsaya numfashinta na fita da sauri ta juyo. Idan kinje karki tsaya palo kikai masa har cikin bedroom dinsa. 'Daga kai tayi ahankali ta juya tacigaba da hawa. #Mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _haske writers association_💡 *20* Not edited Dagowa tayi takallesa tana qoqarin tsayarda hawayenta Suna hada ido ya miqe tsaye ya nufi bedroom dinsa batareda yace qalaba ko waiwayenta. Kallon hannunta tayi dake radadi sosai tasaka 'dayan hannun ta share hawayenta ta miqe ahankali taja hular rigarta ta rufe kanta ta nufi qofa ta fice. Tana saukowa ta tararda Carolina a palo tana qoqarin fara aikin gyaran gidan sbd su amah zasu school. Kallonta Carolina tayi cikeda mamakin ganinta tana saukowa daga saman a wannan time din saidai kuma ba abinda yashafi aikinta bane sai kawai taci gaba da aikinta Itama rumanah nauyin Carolina din taji yasa takasa yimata magana ta nufi dakinta tashige. Toilet tashige tayo alwala daqyar sbd ciwon hannunta tafito tayi sallah tana gamawa ta fito ta nufi kicin saidai duk yanda taso tayi aiki kasawa saidai takoma daki ta zauna ta qurawa hannun ido tana tuno yanda ciwon yasamu. Lumshe ido tayi tuno kalamansa"""inada nauyi ne?""" Sai a lokacin mamakin maganarsa yake shigarta Tasake tuno qaqqarfan jikinsa saikuma tayi saurin lumshe idanuwa sbd kunyar ganinsa dataji saikuma taji sanyin qamshin turarensa yashiga hancinta tayi saurin bude ido taga babu kowa zuciyarta ta buga da qarfi. Mikewa tayi ta nufi jikin window ta tsaya Wani sabon qamshinsa taji yashiga hancinta har zuciyarta ta rufe fararen idanuwanta ahankali tareda budesu takoma bakin gado tasake zaunawa har lokacin hancinta da idanuwanta sunkasa daina jiyo qamshinsa Zuciyarta takasa sukuni Rashin sukunin hakan yasata miqe tafito jiki asanyaye ta nufi kicin. Duk yanda taso yin aiki a kicin kasawa tayi sbd rashin nutsuwar datake ciki gashi hannun yafara kumbura saidai batajin zafin kamar yanda takejinta cikin rudu da rashin sanin abinda yake damunta. Kallo Carolina tabitadashi ganin kamar tana cikin damuwa gakuma hannunta daya kumbura cikin tausayawa tace taje daki ta huta tana kwatanta mata da hannu. Murmushi qarfin hali tayi zatayi magana doorbell yayi qara atare suka kalli agogo da Carolina sukaga qarfe bakwai da minti goma, Wanke hannu Carolina tayi ta fito cikin din ta nufi qofa ta bude. Dawowa tayi riqeda leda fara ta kalli rumanah tace taduba mata chips data zuba ta nufi sama. Knocking tayi ahankali saidai ba amsa hartagaji bail budeba harta aje saidai tadawo qasa dashi takalli rumanah tace magani ne batasaniba ko urgent yake buqatarsa gashi bata shiga bedroom dinsa ta miqawa rumanah tace ta taimaka mata taje gurin sultana tafada mata kozata kirasa awaya tasanar masa. Qura mata ido rumanah tayi sbd sanin bata tada sultana idan tana bacci ataqaicema lokacinda take tashi bacci baiyiba saidai zuciyarta na fargaba da idan yana buqatar maganin ne a gaggauce. Karbar maganin tayi ta fito palo ta nufi dakin sultana saidai kuma tasamu kanta da tsayawa cak sbd qila yana cikin wani haline yake jiran maganin. Juyawa tayi ta nufi saman tana qoqarin danne faduwar gabanta harta isa ta shiga palon ta nufi qofar bedroom din tayi knocking. Shiru ba amsa tasake yin knocking din still ba amsa Kasa juyawa tayi ta rabe qofar dakin gabanta na tsananta faduwa hakama takasa tafiya sbd fargaba. Jin shiru sosai yasata qara kwankwasawa cikin nutsuwa tana qoqarin sake kwankwasawa aka bude dakin hakan yasa saura kadan ta fada masa tayi saurin daidaita tsayuwarta tareda sauke kanta qasa daqyar ta furta, Ga saqo aka kawo. Batareda yakalletaba ya karbi maganin cikin maqoshinsa yace, Wait. Cak ta tsaya ya bude ledar yaciro maganin yaduba ya miqa mata. Dagowa tayi suka hada ido danasa dake kafe da ita tasaka hannu takarba hannunta yakalla batareda yaqara cemata komaiba ya rufo qofar. Hannunta daya kalla yasa ta fahimci mai hakan ke nufi takalli ledar maganin tasaki fuska akaro na farko datayi murmushin daya fito daga zuciyarta tun bayan rasuwar iyayenta. Saukowa tayi ta nufi dakinta ta ajiye maganin ta zauna duk bayan minti qalilan tana waiwayowa takalli ledar. Qarfe takwas su amah suka tafi school bayan fitarsu da awa 'daya ya sauko cikin wasu blue black Balenciaga's suit dogon gashinsa a daure qamshin turarensa na annick goutal mai sanyi ya ratsa palon sosai wayarsa ce kawai ahannunsa sbd meeting zaije ba ba asibiti ba saiyadawo zaije hospital din. Itakadaice a palon itama fitowarta kenan cikin doguwar riga ash zata dakin sultana sbd lokacinda ake gyaran dakinta yayi. Sunkuyar dakai tayi sum sum tashige dakin sultana. Tana shiga ta tararda ita zaune kan couch tana waya cikin girmamawa ta durqusa tagaida da kai ta daga mata sbd wayar datakeyi. Tashi tayi tafara qoqarin gyaran dakin cikin dauriya sbd tsananin azabar da hannunta ke mata saidai bazata iya barima sultanar tasaniba. Shigowa dakin yayi da sallamarda shikadai yaji abarsa ya nufi gurin ammyn ya sumbaci hannunta data miqa masa yana cewa, Saba'ul khair ya ammy. Murmushi tasakar masa tareda katse kiran ta ajiye wayar tana cewa, Barka da fitowa yarima maheer. Kallonta kawai yayi batareda ya amsaba yace, Zan fita sainada dawo. Allah yatsare but did you take your breakfast? Kai kawai ya daga mata ya juya haryakai bakin qofar dakin ya tsaya batareda yajuyo ba cikin husky voice dinsa yace, Bani fruits din gaban ammy. Yawu ta hadiye cikin faduwar gaba sanin da ita yake saidai bazata iya dauka da hannu dayaba dole sai biyu gashi batason ammy tasanda ciwonta. Kallonsa ammy tayi cikin mamaki ganin baya tabacin abinda bashi aka kawowaba. Cikin sanyin jiki ta aje pillon dake hannunta ta je gaban ammy ta dauki dan glass bowl din amma tuni hannunta ya gaza bowl din yafadi qasa ya fashe. Da sauri ammy takalli fuskar rumanah din Da sauri ta durqusa zata bada hakuri sultana takalli hannunta cikeda mamaki da kulawa tace, Rumanah hannunki akumbure, Ciwo kikaji shine kike aiki? Numfashi ya sauke a maqoshinsa kafin ya ficewarsa sbd dama abinda yakeson ammyn ta fahimta kenan. Ita kanta tagano dan ammy tasan taji ciwo yasata daukar Abu mai nauyin da bazata iya dauka da hannu dayaba saidai batasan dalilinsa nayin hakanba. Qura mata ido ammy tayi cikin sigar fada tace, Meya samu hannunki ya kumbura haka kamar ma karywa ko targade. Kallon qofar daya fita tayi asace kafin ta sunkuyar dakai cikin sanyi tace, 'Yar buguwace nayi. Yanayinta sultana takalla taga alamun ba gskia tafada mataba sbd tasan rumanah tun tana jaririya saidai tasan bata taba yimata qaryaba. Qofar itama takalla sbd taga lokacinda rumanah tasaci kallon qofar lokacinda maheer yafita kenan yana sane da ciwon, Kodai dama da gangan yasata daukar Abun? Maida kallonta kan rumanar tayi cikin kulawa tace, Menene kika bugu dashi? Qofa. Sake kallonta ammy tayi tasan tabbas ba abinda tafada din bane taji tausayinta yakamata tace, Tashi kije zansa maheer yaduba miki hannun idan yadawo. Miqawa tayi ba musu ta fice sbd zata iya cewa tunda take arayuwarta batasanma ya ake musuba a alamari duk abinda aka sata shitakeyi sbd suma basu taba sata abinda yakaucewa addininta ko lafiyartaba. Abinci taci kadan tasha magani dakuma shafa ta kwanta nan take bacci yayi gaba da ita. Ranar Carolina ce tayi aikin komai ita kadai. Suhailat ta farfado saidai ko motsin kirki da magana bata iyayi komai sai anyi mata koda su amah suka dawo school da yamma tareda sultana suka nufi hospital dubo mum dinsu. Kodata tashi bacci hannun ya sauka gabaki daya babu wani zafi sosai ta sauko gado ta tube tashiga toilet tayo wanka da ruwan zafi sosai hannun da jikinta dayaso kamuwa da zazzabi suka saki tayi sallah ta fito taci abinci nan takama aikin dinner babu bata dogon lokaci suka gama home made pizza sai boiled vegetables da kuma fruits salad din yarima. Itace ke jera abinci a dining din suka shigo Shine agaba hannunsa riqeda riqar suit dinsa ta sama farar long sleeve dinsa kamar yanxune yasata Kallo daya tayiwa hanyar shigowar ta sauke kai tana aje cups din hannun ta. Shi ko kallon inda take baiyiba duk da acikin idon juna suka fara cikin karo ya wucewarsa sama. Dagowa tayi tabi bayansa dakallo yana kaiwa qofa zai shiga ya tsaya cak Tayi saurin dauke kanta shima baijuyoba sai yashige. Ajiyar zuciya tasaki cikin ranta tana qoqarin daidaita numfashi. Ammy dake kallonsu tun shigowarta tasaki numfashi tareda nufar hanyar bedroom dinta tashiga. Wanka yayi yayi sallar magrib yana zaune kan sallayar akayi ishai yafito yaje masallaci dagacan yana dawowa ko shigowa baiyiba hospital yakoma. Kwance take idanuwanta a rufe amma hawayen daya gani yasashi sanin idonta biyu yakalli nurses din dake tareda shi da sauri suka fice. Shafa fuskarta yayi ta bude idanuwanta dasuke jajir ta qura masa ido zatai magana ya girgiza mata batareda yabude bakiba. Share hawayenta tayi daqyar sbd nauyin jikinta cikin tsanani sanyin murya tace, I love you...i love you and pls always remember it even in the future. Lumshe ido yayi batareda yace komaiba ya sunkuya yayi kissing forehead dinta murya daqyar yace, Time to sleep,Gud night. Lumshe ido tayi tareda gyara lullubinta ya sake kissing dinta yafice bayan yaduba file dinta. Koda ya isa gida babu kowa a palo sai sultana itama dan tanason ganinsa ne. Yana ganinta yasan dawowarsa take jira yayi kissing hannunta yace, Gud night ammy jeki kwanta nadawo. Murmushi tayi tareda miqewa ta fuskanci qofar bedroom dinta harzata wuce tace, Gobe inason kayi mana booking flight zamu wuce Libya nida rumanah zuwa jibi, Kuma inason kafin natafi da ita tasan matsayin aurenta sbd idan munje ba dawowa zamuyiba acan inason tasamu sabuwar rayuwa dan haka kanada zabin iya sauwaqe mata kafin jibi muwuce. Tana gama fada bata juyoba ta shige dakinta. Cak ya tsaya bakin stairs din tun lokacinda tafara magana harta gama yana waiwayowa tana shigewa. Qofar dakinta yakalla kafin ya haye yana isa daki ya kashe wayarsa data damesa da ringing batareda yaduba mai kiranba. Tubewa yayi yafada toilet yayo wanka yana fitowa yagama shirin kwanciya ya kwanta. Gari na wayewa ya qarfe tara saura ya sauko cikin shirinsa sbd yanada tiyata har biyu yau. Motsi yaji dakinsu amah yasa ya tsaya tareda waiwayo qofar tareda tunanin meyasa basu tafi school ba har time din. Tura qofar dakin yayi daidai zata fito saura kadan suyi karo tayi sauri matsawa gefe cikeda jin nauyin rigar dake jikinta ta bacci sbd ganin Carolina taje kaisu amah school tareda driver yasa take gyaran koina kafin caro din tadawo ta rage aiki. Qura mata ido yayi tsawon mintuna kafin yakalli hannunta ya dauke kai yafice ko gaisuwarta bai tsaya amsawaba. Saidata tabbatarda ya fice ta dago kai tareda kallon qofar ta daga hannu daqyar taci gaba da aikinta. Bayan tagama gyaran dakin sultana harzata fita cikin kulawa takira sunanta. Dawowa tayi ta zauna gabanta cikin ladabi ta amsa. ki shirya gobe insha Allah zamu wuce Libya, Rumanah duk Wanda qaddara da jarabawar ubangiji tasama ya rungumeta da imani Allah baya taba bari ya wulaqanta shiyasa nake miki kyakkywan zato sbd ke mai hkr da yarda da qaddarace dan haka ki yarda da qaddarar dazatazo miki dangane da aurenki insha Allah zaki samu kwanciyar hankali da kwakykyawar rayuwa Libya. Gyada kai tai jiki asanyaye sbd dama tasan aurenta bamai dorewa bane. Miqewa tayi ta fice. Tausayinta sultana taji saidai tasan raba auren shine yafi a rayuwar rumanah din sbd maheer bazai taba daukarta amatsayin mataba dan haka gwara ya sauwaqe mata su tafi can ko karatu tasamu tayi har Allah yakawo Wanda zaisota sbd tasan sunyiwa rayuwar rumanah illar da har abada basa fatan tasan sune sukayi mata wannan illar dan kuwa qiyayyarsuce zata ture girmansu a idonta shiyasa takeson ta nesantata ma kwata kwata da mineelik idan tana tareda maheer batai nesa da mineelik ba kuma shikansa idan yagano wannan sirrin saiya tsani sultan da ita kanta mahaifiyarsa. Rumanah na fitowa tacigaba da ayyukanta jiki asanyaye harsuka gama ta nufi daki tayi sallah azahar tananan zaune Shiru akai la'asar tayi ta fito suka hau aikin abincin dare. Suna gamawa Carolina ta nufi dakin suhailat tafara aikin gyara sbd washe gari da safe akace za'a sallamota tadawo gida. Itadai rumanah Suna gama girki ta nufi dakinta tayi alwala tayi sallar magrib tana idarwa tafara hada dukkanin kayanta ta shiryasu a akwatinanta biyu tana gamawa ana kiran sallar ishai tasako wata alwala tazo tayi sallah. Bayan tagama abinci tafito taci daqyar sbd ko yunwa ba bataji ta dauki apple daya takoma daki. Tana shigowa ta tube tashige toilet tayo wanka ta zauna sanyaye gaban mirror spray na Prada tadaure dogon gashinta ta zauna zugum. Qarfe takwas su amah sukai dinner Carolina tashige dasu tayi musu wanka sukai shirin bacci kafin suka fara karatu da tab dinsu daganan kowannensu bacci yayi gaba dashi. Sultana sai qarfe tara da rabi tayi dinner sbd ganin maheer baidawo da wuriba. Tana zaune palon tana kallon news qarfe goma da rabi yashigo yana waya. Ganinta zaune yasashi dakatarda wayar ya kashe gaba daya ya zauna gefenta yana gaidata. Ciro komai na tafiyarsu yayi ya miqa mata sosai gabanta ya fadi da ganin itada rumanah nedai zasu tafi, Duk da wani sashe tanason raba auren amma batayi zaton zai barsu su tafi tareba tayi zaton itakadai zai siyowa ticket din. Karba tayi tareda ajewa gefenta tace, Wane time ne flight din? 9:00am""""yafada yana miqewa. Abiyoka da dinner dinka? Girgiza kai yayi batareda yajuyo ba yace, Abani fruits kawai. Ajiyar zuciya tasauke sbd zancen dazata fada amma ta daure tace, Idan takawo ka rubuto mata sallamarta sbd nunawa sultan sheda nan gaba. Juyowa yayi yakalleta kafin ya juya ya wuce. Yana shiga dakinsa tubewa yayi yafada wanka. Dakanta ta isa kofar dakin rumanah din ta tura ahankali tashiga da sallama. Miqewa tayi da sauri ganin sultana dakanta tazo kiranta cikeda kunya dajin nauyi ta durqusa sbd rigar bacci kawai ajikinta. Ganin tanajin nauyi yasata dauke kai tace, Kije ki kaiwa maheer fruit. To ammy'""""tace ahankali cikin nutsuwa. Idan kin kai kindawo inajiranki adakina. Sake gyada kai tayi. Saida ammyn ta fice ta miqe ahankali tareda daukar doguwar riga mai ma6alli biyu agaba da hula tasaka tafito ta nufi kicin. A qaramin tray ta zuba ta dauki qaramar wuqa ta nufi saman. Sanin baya palo yasa ta murda tashiga ta isa qofar bedroom dinsa ta daga hannunta dake rawa tayi knocking ahankali. Jin shiru harso uku yasata murda tashiga Duhune sosai adakin shiyasa ta tsaya cak tsakiyar dakin. Ba zato taji anriqo hannunta tayi saurin rintse ido numfashinta na fita da sauri. Bedside lamp ya kunna tagansa tsaye gabanta cikin sanyeda dogon wandon bacci fari qal amma baisaka rigaba murdadden jikinsa a bayyane ya kafeta da lazy eyes dinsa tuni jikinta yasake daukar rawa ta aje tray din kan table din tsakiyar dakin ganin zai kufce mata. Yana ajewa ta Juya taji hannunsa yariqo nata ta tsaya cak. Dawo da ita yayi ta baya ahankali bayanta yahadu da qirjinsa. Rintse ido tayi numfashinta na tsananta fita ya zura hannunsa daya ya balle botins din rigarta lokaci daya ta zame qasa ta fadi Sake rintse idonta tayi da qarfi amma ko hannu daya bata daga. Juyo da ita yayi suka fuskanci juna yana kallon fuskarta yasa hannu ya zame rigar baccinta Rigar na barin jikinta tasaki kuka ahankali ya jawota yasaka cikin jikinsa lokacin kukanta ya tsananta Sai kawai ya dauketa ya nufi gadonsa da ita akaro na farko ya hada bakinsa da nata. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *21* Not edited Sanin batada ikon gardamawa yasa bata gardamaba ta rintse idanuwanta ahankali tareda Jan wani irin numfashi jin hannuwansa sun sauka a qirjinta, Sakin bakinta yayi ahankali ya dago lazy eyes dinsa yakalli idanuwanta dake rufe Ya kai bakinsa saitin kunnenta ya furta mata wata kalma ahankali ta bude jajayen idanuwanta sai cikin nasa ta lumshe ido tasake budewa yakai bakinsa ahankali yayi kissing idonta na dama tareda cusa kansa cikin wuyanta yana giga mata dogon hancinsa nan tsigar jikinta duk ta miqe Yasake dagowa ya kalleta hannuwansa na 'dago masa kanta idonsa cikin nata ya Dora bakinsa anata ta rufe ido ahankali sbd jin inda hannunsa ya nufa. Duk yanda takeda juriya saidata zubarda hawayen wahala sosai musamman data tabbarda ta fita daga cikin sahun 'yan mata har abada. Lumshe idanuwanta tayi hawaye suka gangaro tareda kallon qofar bathroom dinda yashiga. Har lokacin jin hannunwansa da kisses dinsa takeyi ajikinta Wanda suke qoqarin ruda mata kwakwalwa saidai ko tashi bazata iyayiba sbd ba qaramar gajiya ya sauke akantaba ta rufe ido bacci yayi gaba da ita ahankali. Qurawa kansa ido yayi ta cikin mirror tareda rufe ido yabude yasake kallon fuskarsa ya fitarda numfashi tareda mamakin kansa da yanayin dayakejin kansa. Wanka yayi yafito daure da towel batareda yakalli gadon datake kwanceba ya nufi gaban mirror yayi amfani da hand dryer ya busarda gashinsa ya saka wasu kayan baccin ya nufi gadon. Kwantawa yayi ya qurawa fuskarta datai jajir ido dagayen eyelashes dinta duk sun nannade da hawaye sbd kukan datayi duk da bamai sauti bane kukan, Suhailat bata taba masa kuka ba idan suna making love ko a first time dinsu kuwa. Rufe idanuwa yayi tareda shigewa dovet. Qarfe takwas sultana ta fito palo cikeda mamakin rashin ganin rumanah din zuwa gaidata. Zama tayi tareda kallon Carolina dake jera breakfast a dining tace takira mata rumanah. Aje aikin tayi ta nufi dakin rumanah da sauri tana budewa bata gantaba tadawo cikin ladabi tace tana toilet. Gyada kai sultana tayi tareda miqewa takoma bedroom dinta. Bayan mintuna tasake fitowa sbd ganin time din tafiyarsu yana matsowa tasake aikawa still tana toilet cikeda mamaki ta nufi dakin da kanta saidai har toilet taduba babu rumanah. Duk inda ake saka ran ganin rumanah Carolina taduba batanan hakan yasa sultana zauna palo cikin fargaba tafara qoqarin kiran wayar maheer amma no answer. Ahankali yabude idanuwansa cikin wata irin kasala yana kallon agogo ya dafe goshinsa cikin mamakin bacci mai nauyin daya hanasa tashi. Gefensa ya kalla yaga har lokacin bacci take dunqule cikin duvet gashinta duk a barbaje kan pillow. Fita duvet din yayi ya sauka gadon ya nufi toilet ganin yayi latti sosai yasa bai tsaya wanka ba yayo alwala yaxo yatayarda sallah. Yana gamawa ya dauki wayarsa daketa fidda blinking alamar kira 11 missed call daga hospital yasan suhailat ce aka sallama Sai 9 missed call daga ammy Miqewa yayi yafada toilet. Yana shiga tailet ta farka ta bude idanuwanta ahankali sbd nauyin bacci dana kukan datayi tana ganin baya dakin tafara qoqarin miqewa ta sauko daqyar riqeda bargo tana rufe jikinta tajawo rigarta ta barci dake tsakiyar dakin yashe. Tana daukar rigar yana bude qofar toilet yafito daure da towel, Kasa dagowa tayi bare ta juyo saima rawa da jikinta keson dauka. Shareta yayi ya nufi gaban mirror yana goge gashinsa sbd Sam bayajin damuwar komai ko gajiya ras yakejin kansa. Ganin kamar hankalinsa baya kanta yasa tayi saurin zura rigarta ta cikin bargon amma still kasa miqewa tayi. Wayarsa tayi blinking yaga kiran ammy ne yayi saurin kallon agogo yaga har tara takusa Sam yamanta da tafiyarsu. Shiryawa yayi cikin white shirt and blue jeansy trouser ya daure gashinsa ya dauki wayarsa ya nufi qofa, Zai fita ya tsaya batareda yajuyo ba yace, Saura 40min jirginku yatashi. Yana gama fada yafice daga bedroom din. Qofar ta kalla bayan ya wuce ta rintse idanuwanta ahankali tareda fitarda numfashi ahankali kafin ta miqe ta taka daqyar ta dauki doguwar rigarta ta zura kan rigar baccinta ta nufi qofa tana qoqarin daidaita tafiyarta duk da zafinda takeji. Saukowa taringayi ahankali harta gama saukowa ta nufi dakinta Tana kaiwa tsakiyar palon tayi ido hudu da sultana zaune ta zuba mata ido cikeda mamaki. Sunkuyar dakai tayi idanuwanta na cikowa da hawayen tsananin kunya da nauyin ammyn. Juyowa sultana tayi ahankali cikeda mamaki takalli inda yake zaune yayi tamkar baimasan da isowar rumanah dinba ya danna kira asibiti. Kasa maida kallonta tayi kan rumanah sai kawai ta miqe ta nufi dining. Jiki sanyaye ta qarasa daki tafada toilet sai kawai tasaki siririn kukan kunya da ciwon da jikinta ke mata. Wanka tayi da ruwan zafi sosai kafin ta lallaba ta fito tayi sallah ta shirya cikin sauri sauri ta fito kai sunkuye. Kallonta ammy tayi cikin sanyin murya tace, Kizo kiyi breakfast mutafi munyi latti. Kai ta daga ta nufi kicin a darare ammy tabita da sabon kallo harta shige tasake juyowa takalli maheer dako gefensu yaqi kallo, Mamakin duniya ne ya taru akanta gashi Sam ko fuskarda zatai masa wata magana yaqi bata bare taji makomar rumanah daga garesa. Daqyar ta iya shan tea da biscuit ta fito daidainan Carolina tagama fitar mata da kayanta zuwa mota. Kodata fito ammy ta nufi waje sbd sunyi latti sosai dan haka ba kowa a palon saishi azaune yana waya Qofa ta nufa riqeda qaramar jakarta tana qoqarin wucesa yakara mata qafa ta kwashi wani mugun tuntube ta fada masa ya aje wayar hannunsa tana qoqarin tashi ya matseta da hannunsa daya tareda kallon cikin idonta ya dauke gira daya cikin izza yace, Ance kitafi ne? Kallonsa tayi da sauri kafin ta Girgiza kai. Hannunta yakamo yasaka mata wata Leda tareda sakinta ya miqe yafita batareda ya waiwayo ba. Bayansa tabi da kallo kafin ta dawo da idonta kan ledar daya saka ahannunta taga magungunane Sake dagowa tayi takalli qofar fuskarta da mamaki. Qofa ta nufa ta fito tana sake damqe ledar maganin a hannunta ta nufi motar da tagansu. Driver ne zai kaisu dan haka dukkaninsu baya suka shiga yana tsaye yana kallonsu aka tayarda motar Dagowa tayi ahankali ta saci kallon gefensa idonsu yashiga cikin na juna tayi saurin sauke kai tareda sake damqe ledar maganin daya bata. Suna fita yafidda key ya nufi hospital sbd tuni suhailat ta damu dayazo daukarta Shikuma ji yake da bayada aiki sosai ammynsa xaibi Libya sbd damuwar sultan yasan haryanxu tana ranta. Yana isa asibitin yahadu da doctor dinda ke kula da suhailat sukayi magana da sauran rubuce rubuce suka nufo gida. Tun ahanya takeson tambayarsa maganar rumanah saidai zuciyarta na gargadin bakinta da furtawa sbd sanin bazaiso maganarba karma ta bata masa rai da kiran sunan an aura masa baiwa. Suna isa gida ta tararda komai fes tashiga dakinta tayi wanka ta shirya cikin simple kaya marasa nauyi ta nufi bedroom dinsa. Cikeda mamaki ta tsaya tsakiyar dakin tana sake bude hancinta sbd dakin wani qamshi yakeyi na dabam Wanda ta tabbar bana maheer bane. Zama tayi bakin gado ta rafka taguma tana wasi wasin tunani Ganin qamshin zai iya buga zuciyarta yasa ta miqe tabar dakin sbd dama bayanan yana ajeta ya koma asibiti. Sun isa Libya da qarfe shida na yamma motocin masarautar mahaifanta sukazo daukarsu cikin qanqanin lokaci suka isa babbar masarautar mai tarin dukiya da adalci Masarautar mineelik saidai ta nuna musu girma da iko tareda dukiya wadda ta hada data mulkin mutanen da ba'a gani sbd dukiyarsu nada alaqa data mutanen daba nasuba amma a fagen adalci da qaunar talakawa da basu yanci basu kamosu ba ko kadan. Saida suka sauka fadar sultan jalaluddeen suka gaidashi tareda gabatarda rumanah amatsayin matar yarima maheer yasawa aure albarka kafin suka isa babban sashen sarauniya salma matar sultan jalaluddeen mahaifiyar sultana zaarah. Sosai aka hau hidimarsu duk da manyanci daya kama sarauniya salma tayi farin ciki da murna sosai ganin rumanah amatsayin matar yarima maheer sbd lurada nutsuwarta. Sashe guda aka ware musu acikin part din sarauniya salma mai daukeda palo da bedrooms guda biyu dasukaji gyaran tsadaddun decor. A babban palon s salma sukaci abincin dare tareda ita kafin kowannensu ya nufi dakinsa. Tubewa tayi tashiga wanka ta jima tana dumama jikinta kafin tafito ta shirya cikin kayan bacci tayi sallolinta harzata kwanta taje ta dauko ruwa tazauna bakin gado tareda fiddo maganin daya bata tasha takwanta cikin qanqanin lokaci bacci yayi gaba da ita. Bacci tayi sosai mai dadi sbd gajiyardake jikinta bata farkaba sai bayan sallar asuba ta tashi tayo alwala tayi sallah tasake komawa ta kwanta. Qarfe tara ta tashi tayi wanka tashirya tafito cikin doguwar riga black mai adon red sequence stones. Dakin sultana ta nufa ta tararda ita tana waya tajira harta gama ta gaidata cikin girmamawa. Cikeda kulawa sultana ta amsa tareda cewa, Ya jikinki? Shiru tayi takasa bata amsa sbd nauyi. Shikenan tashi kije zansa afara kulawa dake harkiji sauki sosai sbd haryanxu jikinki bai nuna kin warkeba. Kamar munafuka ta fito sbd tsananin kunya da nauyin ammyn datake ji musamman data riga tasan tabbas ammy tasan meya faru tsakaninsu. Kodataje gaida s salma acan tayi breakfast dinta har akazo kiranta ta tashi tabisu tanaji tana gani aka hau gyaranta da gashinta kullum cikin sakata cikin ruwan zafi da wasu irin magunguna ake kuma kullum sai anbata 'danyar madara tasha cup daya da safe gashi aiki ko daya anan batayi saidai idan taji jikinta yayi tsami da yawa taje dakin sultana tahau aikin gyara mata kayan wardrobe da wankin toilet duk da akwai masuyi amma wani lokacin tafison tanayi. Satinsu biyu tasaba sosai da kowa, Sultana mamakin rumanah takeyi bata taba tunanin zataga rumanah tasake hakaba shiyasa ba bata lokaci tasa aka dauko wani Mexican malamin wata collage yana zuwa koya mata karatu. Sosai tayi fresh abinta ta dire dakyau kyawunta tuni yaqarasa bayyana sbd Hutu da gyaran da ake mata kamar kullum. Wanka tafito ta shirya cikin kayan bacci riga da wando tazauna bakin gado tareda jawo bedside drawer taqurawa ledar da kullum saita kalla ido tareda lumshe fararen idanuwanta tanajin hannunsa ajikinta lokacinda zai saka mata ledar ahannu. Sake lumshe ido tayi tareda zamewa ta kwanta ahankali tana jin wata irin kasala. Sosai ta warke takoma tamkar batai ciwoba sun cigaba da rayuwarsu kamar da tuni tafara zuwa aikinta hankalinta kwance sbd ganin maheer yamanta da wata maganar aure da aka daura masa, Abinda yake damunta yake hana mata bacci wani bi 'dayane, Maheer Sam bai cika nemantaba kamar da ataqaicema yarage sha'awa sosai sbd wasu lokutan tana lure da inda baya taba mata da yanxu yana tabawa saidai ita Sam bataso musamman nonuwanta Sam batason yana yawan tabasu sbd batason suyi laushi da wuri gashi dama shayarwa tafara lausar mata dasu. Ada Sam basu damesaba shima amma yanxu yanason tabawa tarasa meyasa hakan. Wannan karon sbd ganin uwar datasha dakuma tiyatar da akai mata yasa tayi allurar shekara biyu sbd tahuta mahaifarta tasake qwari. Fitowarsa wanka kenan daureda towel wayarsa tayi ringin yakalli wayar kamar bazai daukaba saikuma ya daga. OK kawai yace ya aje wayar ya shirya cikin kayan shan iska ya sauka. A palo ya tararda baqon nasa yadauki remote yana canza tasha yace, Uhumm. Gyara zama mutumin yayi cikin girmamawa yace, U wanted to see me sir. Batareda yakallesaba ya karbi coffee dinda suhailat ke miqo masa murya a dake yace, I need a first-class vip ticket...... Kallonsa suhailat tayi da sauri cikin mamaki tace, Zuwa ina? Libya"""yafada kai tsaye yana sipping coffee dinsa idonsa nakan TV. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *22* Not edited Da sabon mamaki tasake kallonsa, Libya? Amma baby mezakajeyi a Libya yanxu? I mean is everything OK?...... Dakatawa yayi dashan coffee din ya ajiye tareda juyowa yakalli gefenta cikin izza yace, Ammy na Libya kike tambayan mezanje yi acan?unbelievable. Miqewa yayi yabar palon sbd bayason damuwa da tambayar dazeta iya bata ransa. Bayansa tabi da kallo cikeda mamaki saidai batajin dadin tambayar datai masaba itama sbd mahaifiyarsa nacan baikamata ta tambayi mezaije yiba. Miqewa tayi tabisa dan basa hkr saidai koda taje waya yakeyi haka ta zauna jiran yagama. Zaune suke a qaramin palon baqin s salma itada Mr aarib suna karatu harsuka kammala ya kalleta cikin sakin fuska yace gobe bazai samu damar zuwa ba qila sbd yanasaran zaiyi tafiya idan baiyiba zaizo. Gyada masa kai tayi cikin sakewar fuska ita suka fito kusan atare yana sake maimaita mata wasu English words daya koya mata itakuwa sbd ta sake fahimta bakinsa ta qurawa ido tana daga kai ahankali fuskarta asake sbd ba laifi sunsaba da Mr aarib. Tab dinda ake mata karatu da ita ya miqa mata ta amsa tana murmushi tace, Thank you. Cikin jin dadi yace, Ure welcm. Juyawa yayi ya fice ta nufi qofar palon s salma na gaba tashiga har lokacin fuskarta daukeda murmushi tana shiga palon ta tsaya cak tareda juyawa da sauri sbd qamshin dataji yacika palon. A fuskarsa idonta ya sauka yana zaune yana mgn da s salma gabanta yayi wani irin faduwa wani irin yanayi yashigeta na fargaba ko fuskar gaidasa bata ganiba ta hadiye wani yawun fargaba ta daga kafa daqyar ta isa gabansu kanta a sunkuye ta gaidasa batareda yakalletaba ya 'dan daga hannu Juyawa tayi ta wuce sbd yau babu batun fira a gurin s salma. Tana isa palonsu ammy na zaune tana kallon wani English program Zama tayi tareda aje tab dinta tana cewa, Ammy yace qila gobe bazaizoba. Ammy na kallon TV tace, Eh ai gwara karyazo yanxu yajira bayan kwana biyu tukuna sbd maheer dake qasar baku hadu a palon ammee ba? Eh yana can. Murmushi tasaki tareda kallonta sbd jin amsar dan batai cikakkiyar kama da tambayar datai mata ba Maida kallonta tayi kan TV tana cewa, To yayi kyau. Miqewa tayi ta nufi kicin jikinta duk ya mutu tasha ruwa ta tsaya jikin fridge tsawon mintuna tana sauraron bugun zuciyarta daya canza yaqi daidaituwa tun lokacinda idonta ya sauka akansa. Fitowa tayi ta nufi dakinta ta zauna bakin gado tareda jawo bedside drawer ta kalli ledarta tsawon mintuna kafin ta rufe tareda sauke numfashi Gabaki daya tarasa meya dagula mata nutsuwa ta miqe ta nufi toilet tayo alwalar sallar magrib datayi tazo ta tayarda sallah Tana gamawa palo ta fito ta nufi qofar fita dan zuwa gurin s salma saidai tana kaiwa qofa ta tsaya takasa shiga sai kawai ta juyo tadawo tana zama a palon sultana na fitowa ta zauna tana cewa, Yau bazaki gurin ammee bane? Murmushi yaqe tayi cikin sanyi tace, Karatu zanyi. Satar kallonta ammyn tayi kafin tayi magana sukaji qamshinsa yashigo palon tareda sallamarda shikadai yaji abarsa. Fuska ammy tasaki cikeda farin cikin ganinsa. Itakam miqewa tayi riqeda tab dinta kanta asunkuye zata bar palon tana kawowa gurinsa kamar alamara sai tuntube Tab din hannunta ta fadi Sai kawai yatake ya wucewarsa batareda yanuna yasan da itaba bare tab dinta. Cikeda mamaki ammy ke kallonsa tana kallon tab din da screen yayi mugun damage mamakinta meyasa ya taketa dan tanada tabbacin yaganta. Rumanah kuwa tab din taqurawa ido sbd yanayin takawar ya nuna kamar yasan da ita to meyasa? Kodai laifi tayi? Sanin babu ikon tambaya ko sanin dalili yasata duqa ta dauka ta wuce dakinta. Kallonsa ammy tayi ganin baimasan mesukeyiba yasa tace, Maheer baka lura ka take tab din karatun rumanah ba? 'Dagowa yayi ya zuba mata idanuwansa dasukai wani launi ko bude bakinsa yakasa sai kawai ya miqe yace, Zan shige saida safe ammy. Baki sake tasake kallonsa tace, Maheer akwai abinda ke damunka? You don't seems alright, Kodai sultan ne? Ko abinci bazakaciba? Juyowa yayi yakalleta daqyar ya iya cewa, Gud night ammy. Wucewa yayi yabar palon yanufi part din dayake nasa a masarautar tun kafin yayi aure. Bayansa ammy tabi da kallo cikin fargabar abinda yake damunsa. Zaune take gaban mirror ta qurawa tab din ido sbd ko kunnuwa batayiba alamudai sun nuna ta tashi daga aiki kwata kwata. Hawaye ne taji sun ciko fararen idanuwanta sbd zuciyarta datake zargin laifi tai masa qila. Aje tab din tayi ta rufe fuskarta da hannuwanta biyu tanajin damuwar hakan duk da tasan batai laifin komaiba saidai tana bawa kanta laifin koda acikin rashin sani tayisa. Ammy ce tashigo dakin taganta ahaka To itakuma wannan lafiya? Cikin mamaki da kulawa tace, Rumanah meya sameki? Sunkuyar dakanta tayi tareda girgiza kai murya na rawa tace, Bakomai. Bakomai kike kuka rumanah? Dole akwai wani Abu kitashi kije kikaiwa maheer abinci ina jiranki idan kindawo mayi magana amma kam dole da wani abin. Tashi tayi asanyaye tareda gyara zaman hular doguwar rigarta ta fito jiki asanyaye. A babban tray ta jera masa komai ta fito ta wuce zuciyarta cikeda fargaba jikinta har wata rawar tsoro yakeyi amma haka ta nufi inda akace nan ne part dinsa. Batai knocking qofar palo ba ta murda tashiga sbd sanin baya palo a wannan lokacin, Kyawu da tsarin palon takalla koina qamshinsa yakeyi da sanyin AC ta nufi qofar bedroom tayi knocking ahankali tareda budewa sanin bazai taba maganaba ko bada ixnin shiga. Baya dakin shiyasa ta nufi table din dakin kai tsaye ta ajiye tray din tareda bude fridge dindake dakin ta dauko ruwa tazo ta ajiye masa tana juyowa sukai ido hudu yana tsaye bayanta jikinsa ba kaya dagashi sai towel fari wannan karon dogon gashinsa asake ya zuba mata idanuwansa ya kafeta dasu yanda ko motsi zaiyi mata wuya. Rudewa tayi tarasa yanda zatayi sbd hakanma yasake tabbarda akwai abinda tayi sai kawai hawaye suka ciko idanuwanta suka fara gangarowa ta durqusa qasa ta sunkuyar dakai cikin muryar kukan datake riqewa tace, Yi hakuri ina neman afuwar laifina.......sai kawai kuka Mara sauri ya sake mata. Sosai takeyin kukan yana tsaye yana kallonta kamar mai kallon wani show. Matsota yafara yi tayi saurin rintse ido harya qaraso gabanta ya riqo hannunta na dama ya miqar da ita tareda kallon cikin idonta dahar lokacin ke tsiyayar hawaye yamaida kallonsa ga hannunta da dama dake cikin nasa yayi masa muguwar matsar da azaba tasata kallon cikin idonsa da sauri Idonsa ras cikin nata yake kallonta batareda yasake mata hannunba. Sabbin hawaye ne suka gangaro mata ahankali daqyar tasake furta, kayi hakuri.. Sassauta riqon hannunta yayi tareda matsawa baya kadan yana kallon hawayenta dake tsiyaya. Da hannunsa daya ya shafosu yakalla ya matsota jikinsa sosai yakai bakinsa saitin kunnenta can qasan maqoshi yace, Kinyi kama da albinon malaminki da wannan hawayen. Dagowa tayi takallesa ko qyaftawa batayi tana tsaida hawayenta kamar bashi yayi maganarba yaqara qasa da muryarsa yace, Kallon fa? Sauke idanuwanta tayi cikeda kunya tanason zamewa ta fice amma ba hanya sbd ya matseta jikin bango. Cikeda mamaki da wani irin kallo dake nuna annurin fuskarsa yake kallon kunyarta data bayyana fili Yasa hannu ya juyo da fuskarta tayi saurin rufe ido fuskarta dake fidda wani kyallin Hutu yaqurawa ido har zuwa qaramin bakinta dake qirjinta dake gugar nasa ya sake matseta yana zame band 'din dake daureda dogon gashinta Gashinta ya zubo har gefen fuskarta Yasa hannu ahankali ya janye tareda yasake tura kansa cikin wuyanta murya a shaqe yace, Bazaki zubamin abincin ba saiya huce and I don't eat hutaccen abinci. Saurin dagowa tayi takallesa saidai ko juyowa baiyiba ya qarasa kujera ya zauna Akaro na farko da wani sahirtaccen murmushi ya kufce mata Wanda yasa kumatunta lotsawa akan idonsa ya dauke gira 'daya tareda dauke kai. Qarasowa tayi ta duqa ta bude masa tareda daukar ruwan data dauko ta mayar fridge din dakin ta canzo masu sanyi sbd wainnan sun huce. Wayarsace ahannunsa yana duba wani saqo kamar bashine yasata aikinba. Zuba masa ruwan tayi a glass cup ta aje masa ya miqa hannu yakarba ya kurba kadan ya dago yakalleta tayi saurin sauke kai. Cikin nutsuwa yaci abincin kadan kafin yace, I need a coffee. Kwashe kayan tayi tafice dasu cikin sa'a ammy bata palo tashiga kicin ta aje ta hado masa coffee takoma. Yana toilet kodata shiga yana waya ta ajiye tray din ta dauki cup din ta miqa masa yana karba ya hada da hannunta ya riqe yana cigaba da wayarsa kuma bai kalli fuskarta ba. Kan jikinsa ya fixgota ta zauna tacigaba da wayarsa yana sipping coffee dinsa hankali kwance harya gama wayar ya aje coffee din tareda kallonta yace, Me kike jira haryanxu? Da sauri takallesa cikeda mamaki ganin har lokacin matse take ajikinsa ko hanyar tashi babu. Sunkuyar dakai tayi cikin rawar murya kamar zatayi kuka tace, Zantashi..... Sai hawaye. Lumshe lazy eyes dinsa yayi yabude yana bin hawayenta da kallo a kasalance ya daga hannu ya shafo hawayen yana tattara gashin kanta daya barbaje. Sakin kukan datake riqewa tayi batareda sanin dalilin yinsaba, Zagaya hannuwansa bayanta yayi ya rungumeta tareda rufe idanuwansa. Lafewa tayi tana qoqarin goge hawayenta ya miqar da ita tareda zame mata doguwar rigar sama yabarta data ciki ya cirata sama ya suka nufi gadonsa yazura hannu ya kashe lamps din dakin tareda dora hannunsa akan siririyar rigarta ya zame. Kallon agogo ammy tayi taga qarfe goma sha biyu harda rabi tasake fitowa amma Sam rumanah batanan ta aika gurin s salma batacan Sam hankalinta yaqi kwanciya sbd ganin kukanda rumanah din keyi dazu. Hakanan ta hakura takwanta tareda mamakin maheer bama na rumanar ba. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *24* Not edited Sheraton bamako hotel forth floor room 302 shine dakinsa da ako yaushe yake sauka idan yana qasar. Babban suite ne dayaji tsari irin na rayuwar dayakeso akoda yaushe. Zama tayi a darare kan sofa tareda aje handbag dinta tana kallon tsarin dakin. Tun kafin ya isa yayi musu shopping kayan buqatarsu shiyasa yakalli agogon hannunsa yana 6ata fuska . Knocking akayi ahankali sbd gudun kar ayi disturbing dinsu Ga mamakinta ganin tayi ya miqe ya nufi qofar bayan tasan abaya budewa kowa qofa idan kagaji da knocking ne kashigo koka jira amma saigashi yatashi yaje yabude kuma hannu kawai yasa yakarba ya rufe qofar ya aje kan gado yafara 6alle ma6allan rigarsa. Sauke kai tayi ganin murdadden jikinsa yafara bayyana Yana gama tubewa ya nufi toilet. Ya jima yana wanka kafin yafito yabude kayan ya dauki brush da toothpaste yakoma yayo brush yana dawowa ya fitarda turarrukansa da yayi shopping yayi shirin bacci bayan ya fitarda fararen kayan baccin daya siya yasaka ya fidda wayarsa yakira suhailat datun dazu take kiransa. Miqewa tayi itama tashiga toilet tayo wanka ta fito daureda towel gashinta daure tsakiyar kai sbd karya jiqe gurin wanka. Duk wani nauyi da kunyar duniya jitake kamar suna kanta sbd mayen kallon daya tsareta dashi tun fitowarta kuma lokacin waya yakeyi da suhailat. Rigar bacci tagani kan kujerar gaban mirror tadan juyo takallesa ya dauke gira 'daya yana cigaba da wayarsa. Da mamaki take kallon turaren Prada royal pink for women da shine turarenta, Ya akayi yasan sunan turaren datake shafawa gashi tamazo da nata suna cikin handbag. Wanda ya siyo din ta shafa ta dauki rigar tadaga batai mamakin ganin yanayin rigarba datafi kama da babu sbd tun a mineelik da ake sakata sakasu tasaba dasu. Daga zaunen ya miqa mata hannu na musu tazo ya jawota ya ajeta kan cinyarsa ya zare ribbon 'dinda ke 'daureda gashinta gashin ya zuba yacigaba da wayarsa da suhailat yana cusa hannunsa cikin gashinta zuwa wuyan rigarta. Cikin nutsuwa suhailat tace, Zan kiraka gobe insha Allah gud night. Aje wayar tayi tareda rintse ido da qarfi hawayen dasuka ciko mata suka gangaro kan fuskarta sbd yanayin yanda maganarsa ke fita qasa sosai ta tabbarda akwai abinda yakeyi da matarsa dan mum ta sanarda ita da rumanah yaje. Share hawayenta tayi tareda miqewa ta nufi 'dakin yaranta takwanta kusada fammah tareda jawota jikinta a hankali tace, Ya Allah kabani ikon juriya da adauke kai kan abinda bazai shiga haqqinaba nima kodan karna barwa 'yayana abin takaici da kunya. Rumanah dake lafe jikinsa ta 'dago takalli fuskarta dake kallonta qasa qasa da murya yace, Kinsa matata ta ajemin waya for the first time banine na aje mata ba. Wani irin lumshe idanu tayi Wanda yasashi kafeta da ido kafin yakai bakinsa kunnenta qasa qasa yace, Are you trying to seduce me da wannan idon? Qanqamesa tayi qarfi ba shiri sbd tsananin kunyar da maganar ta bata ya lumshe ido yana sake shigar da ita jikinsa yace, Karki damu suhailat is kind hearted ba duka zata hanaki mijintaba. Miqewa tayi da sauri zata bar jikinsa yasake dawo da ita ta fado masa ya matseta suna kallon juna fuskarsu daf da juna har dogayen hancinsu na gogar juna. Wani irin murmushi tasakar masa akaro na farko Bakin dayayi smiling din yakalla kafin yakalli cikin idanuwanta da itama nasa take kallo ya daga mata gira 'daya sai abin yasake sata murmushi Daqyar ya furta nifa mijin aurene. Rufe bakinta tayi da sauri sbd wannan karon murmushinta dariya yaso zama takalli cikin idanuwansa dasuka riga suka bayyanarda kasalar dayake ciki murya qasa qasa tace, Sorry. Murmushin gefen baki yasaki ahankali tareda 'dan juyar dakai Cikin shagala da murmushinsa da bata taba ganiba takai hannunta kan kumatunsa ta shafo Tana murmushin dake fitowa tun daga cikin zuciyarta. Dafe hannunta yayi tareda dora hancinsa kan nata yana kallon cikin idonta ya dora bakinsa kan nata suka lumshe idanuwa atare tareda qara matse junansu musamman ita dataji hannunsa cikin rigarta Sun jima a sofa suna abubuwansu kafin suka nufi gado dama tun a sofa akayi wurgi da rigar baccin dake jikinta. Qarfe shida na safe ta fito wanka daureda towel gashinta ya mammanne mata a gefen fuska yana tsiyayar ruwa ko gaban mirror taba isaba ya fito daga toilet din shima yana tsane kansa dake jiqe ya suka tsaya gaban mirror yakalleta ta cikin mirron ta 'dauke kai tana maqala maqala hand dryer datun a jiyan da ita yayo shopping. Ita tayi drying masa kansa sbd yanda ya zauna ya baice komaiba yasata tasan itace zatayi masa. Saidaya shirya tsaf kafin tasamu damar shiryawa cikin wani royal blue skinny armani jeans daya matuqar kama hips dinta harzuwa qasanta ya lafe ya matuqar fidda shape dinta sai wata farar Louis Vuitton shapeless chiffon top sai gashinta data saki sbd bayan ta daure ya zare mata band alamar bayason hakan tayi mamakin yanda yasiyo kayan bayan itadai bata taba saka irinsuba saidai batada wani zabi arayuwa sai abinda yace ko ya nuna buqata. Shima blue armani jean da farar Louis Vuitton wideneck ce ajikinsa sai gashinsa daya saki bai daureba sai qamshin turarukansu dake tashi cikin sanyin AC na dakin. Breakfast aka kawo shidai black tea da toasted bread kawai yaci itakuma taci fried egg da vegetables sai fresh milk da ammy tasabar mata dasha kullum. Qarfe bakwai suka fito bayan ta 'daura kimono black akan kayanta wadda ta qarawa shigarta da jikinta kyau suka fito hannunta na cikin nasa. Babu Wanda yadamu dasu baresu da ko fuska babu daga gurinsa ita kuwa Sam batada damuwa akan duk abinda yanuna. Mota suka shiga babu 6ata lokaci suka bar bamako sai airport sbd tun jiya sunyi bankwana dasu mum. A jirgi wannan karon tsuru tayi sbd tsananin ciwo da nauyin da qafafunta suka fara yimata. Kallo 'daya yayi mata yakalli qafafunta dayaga tana kallo kamar zatayi kuka. Kallon qafafun yayi dan ta cire qafarta daga loafers din dake qafarta yaga sun 'dan kumbura yadawo da kallonsa kan fuskarta yayi mata kallon mintuna uku kafin ya riqo hannunta batareda yace komaiba. 'Dan sanyi taji sbd kobaiyi mgn ba yanxu tana gane abinda yake nufi wannan sigace ta lallashi yake mata. Daurewa tayi tasaki jiki duk da vatajin dadin qafafun. Sai yamma suka sauka direct masaukinsu motar da tazo daukarsu tayi dasu amatuqar gajiye tayi wanka daqyar tayi sallah ko abinci bataciba sai bacci. Wanka yayi shima yashirya yafice bayan yasa ankawo mata abinci batareda yatasheta daga baccinba. Sai magrib ta tashi tana ganin abincin tasan bayanan ya fice ta tashi tayo brush tazo tafaracin abincin tana lumshe ido sbd yunwar datake damunta dama. Saidata qoshi takuna ta tashi tayo alwala tayi sallah tana gamawa tadan zauna tana kallon TV ta nutsu tana sake daukar kalaman turancinda Mr aarib ke koya mata. Lokaci ta duba ta tashi tayi sallar ishai tana gamawa tayi wanka tayi shirin bacci ta kwanta nan take bacci mai dadi yadauketa. Koda yadawo tayi nisa a bacci yayi wanka kawai shima ya kwanta tareda kashe wutar dakin ya dora kansa a pillonda kanta yake ya rufe ido shima bacci yayi gaba dashi. Washe gari bayan yashirya zai fita ya jawota jikinsa yana kallon idonta ya saka mata wayarsa daya a hannu murya qasa yace, Ammy na nemanki idan takira saiki sanarda ita abinda takeson ji. Baki tasaki tana kallonsa harya fice yaqi juyowa kar bashi yayi maganarba to ita mezata cewa Ammy? Ko wayarta ma bazata iya dagawaba sbd kunyar rashin komawarsu bare harta iya mata bayani. Aje wayar tayi tana kallon wayar akai akai hardai takoma tayi baccinta. Kwanansu biyu kullum yana fita aikin dayazo yi shiyasa ta samu Hutu. Yauma sai dare yadawo saidai koda yadawo idonta biyu cikin laushin murya tace masa, Sannu da dawowa. Aje wayarsa da shopping bags din hannunsa yana kallonta kafin yadawo gabanta yana kallon shigarta ta wata red mini dress dake jikinta ya 'dauke gira daya yace, Kinason ki lalatawa Ammy yarone shiyasa kikaqi bari akoma. Zaro ido tayi tareda saurin juya masa baya tana dafe qirjinta da kusan rabinsa yake a bayyane ya zuro fuskarsa ta wuyanta bakinsa a kunnenta yace, Naga bayan tunshigowata ai. Da gudu ta bar gurin ya riqo hannunta tareda dawo da ita ya dauketa cak ya nufi toilet. Ajeta yayi tsakiyar toilet din ya tsareta da ido tasaki boyayyan murmushi sbd tasan manufarsa Hannu tasa tafara cire ma6allan rigarsa har ta kai qarshe ta zame masa rigar ya shiga cikin bathtub yakwanta cikin ruwan sumi tareda lumshe ido yabude ya miqa mata hannu ahankali tazame rigarta ta kama hannunsa tashiga ruwan ta kwanta saman jikinsa. Qarfe uku na dare ta farka da ciwon qafa tun tana daurewa harta zame daga jikinsa ta tashi zaune tareda kunna lamp din gefenta ta kalli qafafunta. Tabasu tayi ta juyo takalli gefensa suka hada ido sbd tun tashinta ya farka. Hawayen datake riqewane suka gangaro mata ya tashi zaune yana kallon qafafun da kai yayi mata alamar tahowa garesa ta fada jikinsa tareda sakin siririn kuka sbd ciwo suke mata sosai jitake kamar zata gurgunce. Jin kukanta yakasa tsayawane yasan ciwonne yayi mata yawa yakai hannunsa ahankali yana matsa matasu ahankali Ta sake shigewa jikinsa tana sauke ajiyar zuciya. Koda gari ya waye kasa tafiya tayi shine ya dauketa yakaita toilet yakuma dawo da ita wunin ranar kusan shine yakeyi mata komai duk da ya duba qafafun yakira Dr vin yayi magana dashi akan maganinda zai mata sbd ba 6angarensa bane. Haryasa ankawo masa maganin saiga kiran Dr vin lokacin tana zaune ajikinsa tana bacci shikuma yana duba wasu takardu. Hello Dr M.A shams I think you should confirm if she's not pregnant first before given her the drugs.... Akaro na farko dayaji zuciyarsa ta girgiza ya qurawa fuskarta ido yaga yanda fatarta take glowing ya daga hannunta yaqurawa tafin hannunta ido take ya rufe ido tareda dafe goshi cikin wani irin yanayi. Ya jima yana kallonta cikin wani irin yanayi da shikadai yabarwa kansa sani kafin ya dauki na shafawa kawai ta shafa mata kadan ahankali kafin ya tashi da ita rungume ajikinsa ya nufi gadonsu ya kwantar da ita kafin ya zauna bakin gadon tareda rufe ido yana shiga tunani. Washe gari koda ta tashi taji sauqi sosai saidai kuma yini tayi duk motsinda tayi idonsa nakanta tayi mamaki dukda tasan kallo a gurinsa ba baqon Abu bane agurinta amma na yanxu ya banbanta. Abinda yafi qara bata mamaki shine yanda yakasa rabuwa da jikinta dole kawai ke tadashi sosai ta lura akwai abinda yake ransa. Bayan kwana biyu ta warke sosai harya fita da ita sukaje wani babban eatery dakuma shopping sbd ganin zama guri dayane yafi saka qafafun ciwo shiyasa akwanakin kullum da inda suke zuwa musamman beach sbd ta lurada yanason ruwa. Satinsu biyu cif suka koma Libya. Da yamma sosai suka iso Motar dataje daukarsu bata dawo gida direct ba saida suka biya wani babban pharmacy aka siya mata magungunan dabatasan na meyeba kafin suka nufi gida. Suna isa taji sabon nauyin ammy yarufeta batasan ta yaya zata hada ido dasuba har gwara s salma suna 'dan wasa wani lokacin. Lura yayi da yanayinta yasaki Murmushin gefen baki kafin yadan ranqwafo yace, Ina gaida ammynah kafin nashigo anjima. Yana fadar haka aka bude masa motar yafita batareda yasake waiwayowaba ya nufi sashen sultan jalaluddeen. Bayansa tabi da kallo tana jinjina alamarinsa kafin aka bude mata ta fito ta nufi hanyar sashen s salma. Sa'ar dataci ammy bata gurinta nan ta zauna tana gaidata tareda kasa cewa komai duk tsokanarda s salma din ke mata saidai kawai tayi murmushi qarshe dai miqewa tayi ta nufi palonsu. Da sallama tashiga ammy dake zaune tasaki murmushin murnar ganinta tana cewa, Munsamu dai yau kundawo. Sauke kai tayi tana Murmushin dole sbd kunya tace, Ammy ina wuni? Murmushi ammyn tayi tace, Lfy kalau rumanah jeki ki huta nasan agajiye kike idan kinhuta saimu gaisa. Babu musu ta nufi hanyar dakinta masu aiki biyu suka bita da luggage dinta ammy tabisu da kallo wainda sukaje bada kayaba saigasu da akwati. Ajiyar zuciya tasauke lokacinda tashiga daki ta zauna sbd Allah yagani taji kunyar ammy tun kafin su dawo. Wanka tayi tai salloli kafin ta fito ta nufi dakin ammy nan dai suka sake gaisawa ammyn nasake tambayarta jikin mumyn suhailat. Suna cikin fira sama sama saigashi yashigo babu kunya ya nufi ammyn kai tsaye ya 'dan rankwafa yayi kissing forehead dinta yana cewa, Ammy barka da hutawa. Ya zauna kusada ita tareda yiwa rumanah wani irin kallo tayi saurin Sauke kai sbd ganin ammy. Kasa 6oye mamakinta ammy tayi tace, Maheer baka taba zuwa dubiya irin wannan ba kokuwa dan kaje da 'yata ne? Murmushi yayi batareda ya'dago daga duba wayarsaba yace, Tambayi 'yartaki. Da sauri rumanah ta miqe ta nufi qofa ta fice tana mamakin iya cabo maganarsa. Kallon ammy yayi yace, Gobe insha Allah zan koma. Kallonsa tayi tace, Allah yakaimu. Fira suka dingayi sama sama duk da itace mai maganar iyakacinsa kallo sai daga kai sai sa'a yake bude baki yayi wata maganar. Da daddare harta kwanta ta tafito taje kicin ta dauko ruwa sbd wani lokacin tana tashi shan ruwan dare. Kodata dauko ruwan takoma daki kasa bacci tayi ta tashi zaune tareda rufe ido tana kamar daga sama taji qamshinsa acikin dakin ta bude ido da sauri amma babusa ta dafe goshi tareda sake kwantawa ta rufe ido tana fatar bacci ya dauketa. Daqyar ta samu bacci yadauketa kodata farka da asuba da ciwon kai ta tashi ta lallaba tayo alwala tayi sallah. Tana gamawa zazzabi ya kwantarda ita agurin ta kwanta ga sanyin AC amma ta kasa tashi. Jirgin qarfe goma sha biyu zaibi amma tun asuba idonsa biyu yakasa bacci. Ammy data kwana tunanin basa rumanah yaje da ita kokuwa aa tana gama sallar asuba ta fito ta nufi dakin rumanah dan cewa ta shirya sutafi tare Tana shiga taganta kwance a inda tayi sallah yanayin yanda ta dunqule gu 'daya ya tabbar matada batajin dadine. Cikin kulawa ta isa tana kiran sunanta Ta tashi zaune daqyar tace, Ammy ina kwana. Lfy meke damunki? Babu komai ciwon Kaine kawai. Fita ammy tayi taje dakinta tadauki wayarta ta danna masa kira kamar bazai daukaba saikuma ya dauka kai tsaye tace, Kazo yanxu kadubamin ita batada lafiya. Aje wayar yayi tareda lumshe ido ya bude dan yasan za'a Rina. Wanka zai shiga amma ya fasa ya mayarda jallabiyarsa ya fita ya nufi palonsu dan har lokacin gari bai gama haskeba. Koda ya isa palon ammy na tsaye tana jiran shigowarsa palon. Da qaramar murya yace, Sabhaul khair ya ammy. Kai kawai ta daga masa sbd masiffen tashin hankalinda tasamu kanta aciki na fargabar kar ace tunaninta na cikine da rumanah ya tabbata. Dakinta takoma ta zauna jira ganin yashiga dakin tareda turo qofa. Zaune take bakin gado tana ganinsa taji idanuwanta sun ciko da hawayen muguwar kewarsa datayi batasan lokacinda ta miqe ta fada jikinsaba ya lumshe ido tareda qara shigarda ita jikinsa. Jin zafin jikinta yasashi dagota yakalleta cikin wata irin murya yace, Qafan ne? Girgiza kai tayi tana kallonsa. Da gira ya yayi mata tambayar then wat is it. Zamewa tayi taje bakin gado ta zauna cikin sanyin murya tace, Ciwon kai. Zama yayi bakin gadon tareda dago fuskarta yayi kissing bakinta yasake taba jikinta yaji zafin Baice mata qalaba ya zare rigarsa tareda ajewa ya kwanta kan gadon tareda lumshe fararen idanuwansa Saidata aje numfashi ahankali kafin ta nufi gadon ta hau tashige jikinsa tareda qanqamesa sukai shiru kowanne najin bugun zuciyar dan uwansa yanaji zafin jikinta na shiga jikinsa ahankali ya saki wata irin boyayyar ajiyar zuciya. Daga haka baccin dabasuyiba adaren ya daukesu ammy dake zaman jira tashigo dakin tayi saurin juyawa ganin yanda sukai bacci hankali kwance. Kasa zama tayi ta kasa tsayuwa sbd idan har cikineda rumanah to yazama dole aciresa sbd tsoronta na bata rumanah zata iya haihuwar namiji Wanda hakan shine babbar masifar dazata tono abubuwa ciki harda yanda iyayen rumanah din suka rasu. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *23* Not edited. Qarfe hudu na asuba ya farka yabude idanuwansa daqyar sbd bacci da kasala, Fuskarta dake kwance kan pillow daya datasa fuskar yakalla bayan ya kunna lamp yaga hawaye duk sun bushe mata a fuska sbd kukan da tasha adaren. Shafa fuskarta yayi kafin ya tashi zaune ahankali ya sauko gadon. Toilet yaje ya kunna ruwan dumi a bathtub yadawo dakin, Sanin koda ta tashi ba lallaine ta iya tafiya ba sosai yasa babu wani bata lokaci ya zura hannu cikin bargon ya dauketa ahankali ya nufi toilet. Cikin ruwan yafara shiga tana hannunsa kafin ya kwanta tareda kallon fuskarta datake cusawa qirjinsa sbd tsananin kunya alamun ta tashi kenan tasan meke faruwa, Tsananin kunya yasa takasa rabuwa da jikinsa saima sake shigewa datayi sbd babu abinda ke jikinta. Shikuwa lumshe idanuwansa yayi ya rufe cikin wani irin kwanciyar hankali sbd 'dumin ruwa dana jikinta dasuke ratsasa arayuwarsa bai ta6a samun body contact ba kamar wannan sbd ruwan dasuke ciki sun qarawa fatarta data hadu datasa laushi. Gashinta da rabinsa yashige cikin ruwan ya kamo tareda dawo dashi kan kafadarta sbd duniya jiqaqqen gashi na burgesa sbd it's so sexy and attracted. Shower ya zura hannu ya kunna nan take gashinta yaqarsa jiqewa suna kwance cikin ruwa wata irin ajiyar zuciya ya sauke a 6oye kafin ya dago fuskarta yana kallon idanuwanta dasukai laushi yayi kissing dinsu ahankali yana shafa mata kumfa a wuya har zuwa qirjinta Wani irin kasalallen numfashi taja tareda rufe ido tana qanqamesa sbd ba qaramin waiwayi hakan yamataba. Yanayin yanda ta lumshe idanun kamar bazasu lumshe ba yasa yaji jikinsa na neman saki yasake kallon idanunta da nasa lazy eyes din itama shitake kallo amatuqar gajiye da baccin dabai ishetaba. A lalace dai sukai wankan saidayaga lokacin sallah na wuce masa yayi wankan tsarki yafito itama daqyar ta iya wankan sbd kasala da bacci tana fitowa taga hand dryer dinsa dake maqale jikin socket a kunne 6oyayyan murmushi tasaki sbd tagane me hakan ke nufi ta isa gaban mirror ta zauna tafara drying kanta tana gamawa tasaka kayanta tayi sallah tana idarwa anan ta kwanta sai bacci. Koda yashigo dakin yaganta aqasa ya jima yana kallon gashinta dabata busar dashi sosaiba"""meyasa koyaushe takeda sa'ar yin abinda nafiso?? Daukarta yayi ya kwantar a gadon bayan yazare mata doguwar rigarta yabarta da rigarta ta bacci. Qarfe tara da rabi ta farka ta bude idanuwanta dasukai nauyi tasake lumshewa ta bude sai akan kyakkyawar fuskarsa dake daf da tata, Qura masa ido tayi tundaga kan idanuwansa har zuwa hancinsa Akan bakinsa ta tsayar da idanuwanta tana tuno laushinsu da qamshinsu...rufe idonta tayi cikeda kunyar tuno aikinda bakin yayi. Juyawa tayi zata sauka gadon can qasa taji yace, Kingama kallon? Zaro ido tayi cikeda mamaki kafin ta sauka gadon da sauri saidai tuni yadawo da ita ta fado masa ya riqe qugunta yana kallon fuskarta dake 6oye yanayin datake ciki. Jin hannunsa cikin rigarta yasata kallonsa amma Sam kamarma bashine yasa mata hannunba. Yanayin yanda yake wasa da cibiyartane zuwa qirjinta yasa numfashinta sauyawa tafara qoqarin zamewa amma tuni motsinta yasake basa damar jinta dakyau. Zame rigar yayi ya juyar da ita takoma qasansa ya dora lips dinsa anata yana sake lalabeta tuni tafara kukan tuno wuyar datake sha. Qarfe goma ta fito wanka daureda towel dinsa gashinta na tsiyayar ruwa farar fatarta sai wani irin sheqi takeyi, Wani irin kallo yabita dashi yana latsa wayarsa da fararen idanuwansa. A sukwane ta qaraso ta busarda gashinta ko 'daurewa batayiba tasaka kayanta tajuyo a sukwane ta 'dan saci kallonsa taga hankalinsa yana kan wayarsa. Daidaita muryarta tayi cikin sanyi tace, Ina kwana? Dagowa yayi yakalleta yaga yanda tayi nar nar da ido ya 'daga mata kai ahankali can qasan maqoshi yace, Ina gaida ammy kafin nashigo. Kallonsa tayi gabanta yayi mugun faduwa sai a lokacin ta tuno ammy tace taje tadawo tana jiranta. Juyawa tayi ta fice jikinta na sakewa da wani irin nauyin ammy Dan batamasan mezatace mataba. Gurin s salma tafara zuwa kamar mara gskia ta gaidata tana sunkuyar dakai Da mamaki ta amsa sbd sanin babu irin wannan gaisawar atsakininsu sbd sunyi sabo sosai suna sakewa da juna. Miqewa tayi ta nufi qofar palonsu tanata kame kame hakadai tayi sallama ta shiga Ammy dake zaune palon ta amsa tareda mata kallo 'daya ta mayarda kanta kan abinda takeyi. Ammy ina kwana'""ta furta muryarta na rawa. Lafiya klau rumanah kintashi lfy? Kai tadaga sbd babu bakin bada amsa Ammy tajuyo tadan kalleta taci gabada canxa channel. Hanyar daki ta nufa tana tafiya a hankali ammy tabi bayanta da kallo tareda sakin murmushin tausayinta. Kaya tacanxa zuwa doguwar riga mara nayi da hannu tafito taje dining ta hada tea kawai tasha takoma daki tana kwantawa sabon bacci yayi gaba da ita cikin nutsuwa. Bai fito part dinsa ba sai lokacin sallar azahar daga masallaci ya nufo part dinsu yana shiga ammy na qoqarin zama kan dining suka zauna tare yana gaisheta cikin kulawa. Ita kunyarsama takeji yanda yayiwa yarinya son ransa amma ya fuske kamar bashiba. Abinci suka faraci tana sake tambayarsa su amah saidai ya gyada kai kokuma gajeruwar amsa. Fitowa tayi palon tana ganinsa taso juyawa ammy tace, Rumanah bani sabuwar madara a fridge. To tace ta nufi kicin tadauko tana kawowa ta zuba mata a glass cup ta miqa mata. Daukar wani cup din tayi ta zuba shima ta miqa masa cikin ladabi. Hadawa yayi da hannunta ya riqe tayi saurin kallonsa tana qoqarin zame hannunta ta saci kallon ammy Sultana tayi saurin 'dauke kai tana kai cup bakinta. Daure fuska yayi saidata fara tsiyayo hawayen kunyar ammy data tabbarda tagansu kafin yasaketa kamar baisanma meya riqeba. Da gudu gudu ta isa daki sai kawai ta cusa kai cikin qafafunta tana share hawayenta. Saidata tabbatarda yabar palon tafito ta tsakuri abinci sbd ko wata yunwar kirki bataji takoma daki ta zauna sbd 6oyo takeyiwa sultana sbd kunyar data hanata sukuni. Da daddare saurin yin baccin tayi sbd karma tasamu dalilin zuwa dakinsa, Washe garima da wuri tayi bacci Amma baccinta rabi rabi tayisa qarfe tara ammy tace takai masa breakfast kansa na ciwo babu wani wasi wasi ta hada ta nufi part dinsa tana shiga tagansa dunqule cikin bargo ga AC daya qure duk sanyi yakama dakin haryayi yawa. Aje tray din tayi tana kallonsa cikin tsananin sanyin jiki da damuwar ganinsa cikin wannan halin. Qarasawa tayi bakin gadon ta leqa fuskarsa taga idanuwansa a lumshe alamar bacci yakeyi ta 'daga hannunta ahankali ta dafa goshinsa taji babu zafi tasake leqa fuskarsa sai kawai sukayi ido biyu ta zaro ido tareda juyawa da sauri Taji yariqo hannunta cikin kasala ya tashi zaune yana zuba mata idanuwansa dasukai sauya sbd ciwon kan dake damunsa. Sauka gadon yayi ya nufi toilet Tana ganin yashige takalli gadon daya tashi tafara janye bedsheet 'din dake kai dan canxa masa wani duk da baiyi komaiba kamar ma yanxu aka shimfidasa Cikin wardrobe taduba ta dauko wani ta shimfida tagyara gadon tafara gyaran dakin cikin qanqanin lokaci tagyara dakin ta rage AC ta duba taga turaren daki ta fesa nan take dakin yaqara daukar ni'imantaccen qamshi da sanyi mai dadi. Ruwa ta dauko masa a fridge taba juyowa tajisa a bayanta takada juyowa saidai ajiyar zuciya datasaki sbd sanyin ruwan jikinsa dake tabata. Juyowa tayi ahankali tareda kallonsa shima ita yake kallo ido ciki ciki. Ruwan hannunta ya zare yasaka mata towel aciki batareda ya dauke idanuwansa ta cikin nataba Dauke idonta tayi ahankali ta dago hannunta takalli towel din dayasa mata a hannu ta dago takalleta ya dauke gira daya tareda nufar gaban mirror yazauna. Matsawa tayi ta dora hannunta dake kyarma jikinsa tafara goge masa jiki harta gama babu wata magana atsakaninsu. Tana gamawa ta sulale ta fita takoma dakin ammy tadan sake gyara mata duk da masu aiki sunyi gyaran. Tana tsaye gaban wardrobe tana gyarawa ammy kaya yashigo dakin yana fidda wani sanyayan qamshin turarensa White gucci shirt da Blue jeans ne ajikinsa gashin kansa asake yana qyalli. Kusada ammy ya zauna tareda riqo hannunta yayi kissing yana cewa, Good morning ammy. Kallonsa tayi tace, Wuni dai sbd mu munjima da tashi. Murmushin gefen baki yasaki kawai yace, Yau zanyi tafiya zanje Mali mum din suhailat batada lafiya. Kallon rumanah da duk takasa sakewa sbd shigowarsa tace, Kuje tareda rumanah tadubota a maimakona. Yi yayi kamar baijiba ya miqe yace, Nanda 30min zan wuce kuma yau zan dawo. Allah yakaiku lfy. Ficewa yayi ta kalli rumanah tace, Aje jeki ki shirya kinji yace nanda 30min. Tariga tagama sai kawai ta fice tana zuwa ta canxa kaya sbd bata dade da wankaba. Doguwar riga royal blue mai shegiyar tsada stones dinta sai wani qyalli sukeyi tayi rolling gyalen rigar sai wasu black wedges dake qafarta na lady dior dasukaiwa farar qafarta kyau sai handbag dinta da turarene kawai da powder aciki ta fito palo daidai lokacinda akace ta fito. Cikin jin nauyi tayiwa ammy sallama ta fita. A wata black mota tagani sai kyalli takeyi suka nufa aka bude mata baya tashiga yana zaune yana waya hankali kwance babu damuwar komai a fuskarsa. Jan motar driver yayi suka nufi airport. Abinda yafi bata mamaki shine ganin suna zuwa basu aka basu tickets dinsu Kenan the tickets are booked already. Jerawa sukayi har cikin jirgi suka nufi gefen first class suka zauna yayi crossing legs yadauki jarida yafara karatu hankali kwance. Qarfe uku suka isa Miqewa tayi tana dan canxa fuska sbd qafafunta dasukai wani iri Sam yanxu bata iya dadewa zaune sai qafafunta su 'dan kumbura. 'Daga qafafunta tayi taji jiri ya 'debeta Jikinsa tajita ya riqo kafadarta yayi mata wani kallon ciki ciki. Sunkuyar dakai tayi cikin laushin murya tace, Yi hkr. Riqo hannunta yayi cikin nasa dayan hannun kuwa cikin aljihun wandonsa fuskarsa sanyeda shades suka fito jirgin sbd ganin alamar kamar har lokacin jirin bai gama sakintaba. Daga gidansu suhailat mota tazo daukarsu suna isa gidan nan aka fara hidima da farin cikin ganinsu. Sosai iyayen suhailat suka tarbi rumanah babu wani damuwar komai. Daqyar tasake sukaci abinci gaba daya a dining nan takejin su suhailat exam dinsu amah suke jira agama suzo dubiya suma. Dakin mum din suhailat tayita janta ajiki danta sake jikinta saidai takasa sakewa sosai gashi yafita shida dadyn suhailat har magrib shiru baidawoba. Ganin har anyi sallar ishai bai dawoba yasa tacire ran komawarsu ranar. Qarfe tara da rabi yadawo ko shigowa baiyiba dad yabugowa mum din waya yace rumanah tafito sutafi. Da mamaki tace, Badai komawaba a Daren nan? Aa masaukinsa zasu tafi dan gobe flight din qarfe takwas zasubi zuwa labanon akan wani program damukai magana dashi yanxu. OK tace ahankali jikinta na sanyi sbd hakanan tausayin 'yarta ya shigeta saidai tunda bai wulaqanta musu 'yaba bazasuji zafi akan aurensa da matarsaba. Cikin murmushi ta tashi ahankali ta nufi wardrobe ta dauko wasu dogayen rigunan Mali masu tsananin kyau guda biyu ta miqa mata daqyar ta karba tana godia suka fito. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *25* Not edited Zama tayi tareda rafka tagumi cikin zullumi da rashin sanin madafar tunaninta Abu 'daya tasani shine tana tsananin qaunar rumanah kamar itace ta haife musamman a yanxu datake hango soyayyarta mai tsanani a idanuwan Maheer 'dinta saidai duk wannan qaunar da yardar zata rushe tazama qiyayya da tsana mai tsanani idan sirrin rasuwarsu asma'u da bulama ya bayyana ga rumanah abinda bazatasoba kenan. Qarfe goma da mintuna goma sha biyu suka farka yatashi zaune tareda tayarda ita zaune yana gyara mata gashinta daya barbaje. Kallonsa tayi tareda sakin kasalallen murmushi Ya shafi gefen fuskarta tareda bude baki yace, Yaya? Lumshe ido tayi cikin laushin murya tace, Yayi sauki yanxu banajin ciwon kan. Lumshe ido yayi tareda jinjina kai kafin yakalli agogo yace, Ya salam" yana sauka daga kan gadon. Tare suka shiga toilet din dakinta sukayi wanka Wanda yadaukesu dogon lokaci sbd tsayawa shiririta. Koda suka fito kan cinyarsa ya zaunar da ita tana goge masa ruwan jikinsa yana kallon gashinta dake 'digo masa ruwa sbd wasan dasukai acikin bathtub yasa dole suyi wankan tsarki. Riqo hannunta dake goge gashinsa yayi tareda Shafo gashinta har zuwa fuskarta ya zarce cikin towel dinta ya shafo cikinta dake lafe yana kallonta cikin wani irin yanayi da galabaita da zuciyarsa ke ciki. Daqyar ya bude baki cikin wani irin taushin murya yace, I have something precious inside you so daga yanxu bazaki sake ganin albinon malaminkiba sbd gudun daukar jajayen ido da qaton baki. Murmushi zancensa yasa tasaki tareda zare hannunta taci gaba da goge masa gashi batareda tace komaiba. Sake riqe hannunta yayi yana tsareta da ido yace, I will miss this smile dakikeyi danki hanawa suhailat mijinta. Kallonsa tayi gabanta na faduwa sbd jin sunan suhailat yasatajin faduwar gaban ta sunkuyar dakai tareda tashi daga jikinsa ta dauko hand dryer ta jona tafara busar masa da gashinsa mai tsananin laushi. Shidakansa ya shiryata cikin pink gathered neck top da black straight skirt ta Sanya black hula ta fito ta nufi dakin sa ta dauko masa kayan dazai saka takawo masa yasaka suka fito palon hannunta na cikin nasa tanata 6anbare hannunta amma takasa ahaka yajata har gaban ammy dake sintiri a tsakiyar bedroom dinta tana ganinsu tasaki murmushin qarfin hali tana qarajin tausayinsu dan ko ayanxu datake ganin yanayinsu bama zasu iya rabuwa da junaba saidai duk soyayyarsu qila basuda rabon hada zuria sbd bazata so rumanah ta zamto itace zata fara haifarwa maheer namijiba gwara dai wata kokuma suhailat duk da itama bazataso wani Abu yasametaba saidai so sone amma sonkai yafi. Cikin kulawa tace, Rumanah yajikinki?kan yadaina ciwo ko? Kai ta daga tana sake janye hannunta amma Sam kamar bashine riqeda hannunba. Abinci sukaci a dining ammy madai hartafi rumanar jin kunyar abinda maheer din kemata kuma ko ajikinsa tamkar bashine yakeyiba. Daqyar sukaga sungama ammy tarigasu barin gurin tana girgiza kai sbd batasan haka 'danta yake 'dan duniyaba. Ammy na barin gurin takallesa kamar zatayi kuka yazuba mata ido tareda sakin wani miskilin murmushi kafin ya miqe tsaye ya ranqwafa yayi kissing kanta yace, Ki kula. Ya fice yana duba agogon hannunsa sbd lokacin tafiyarsa yayi sosai. Bayansa tabi da kallo hawayen datake riqewa suka gangaro tasa hannu ahankali tashare tareda miqewa ta nufi dakinta ta zauna bakin gado sai kawai siririn kuka ya kufce mata. Yini tayi adaki kwance bayan sallah babu abinda ke tayarda ita ko abinci yau ammy daki tasa aka kai mata sbd ta fahimci halinda take ciki na tafiyar maheer 'din. Da daddare ma kasa bacci tayi harsai kusan asuba ya saceta koda ammy ta leqo taga bacci takeyi bata tadataba sbd tasan balallaine tasamuyin bacci da daddare ba. Koda gari ya waye sosai guraren qarfe goma ammy tadawo ta tararda ita cikin wani zazzafan zazzabi nan hankalinta yafara tashi musamman yanda jikinta yayi wani mugun zafi banda amai babu abinda takeyi Ganin abin na girmama yasata sanarda s salma nan aka kirawo Dr faduwa tazo tadubata tareda fara mata pregnancy test dan karta maganin da baikamacetaba awon farko ciki ya tabbata nan ammy taqara shiga damuwa ga farin ciki ga fargabar abinda zai iya zuwa yadawo. Magani tarubuta tareda Wanda zaita tasamu dan bacci kota huta daga aman. Kallonta ammy tayi bayan fitar Dr faduwa tasauke ajiyar zuciya tareda mata sannu cikin tsananin kulawa da qaunarta. Abinci ammyn tasamu taci daqyar kafin tayi sallah tayi wanka ta kwanta wani sabon baccin yayi gaba da ita. Tunda yatafi bata sake lafiya ba sosai ciwo ya kwantarda ita komai taci baya zama cikinta Duk inda hankalin ammy yake ya ninka tashi drip kuwa tasha ledoji qarshemadai daina samata ruwan akayi. Batasan 'daga masa hankali kokuma shiga haqqin suhailat shiyasa bata fada masa saidai duk yanda taso tare alamarin fin qarfinta yayi dan yanxu wata biyu da tafiyarsa ga mamakinta cikin harya fara tasawa gashi har lokacin ko zaman arkiqi bata iyayi koyaushe akwance take. Gyara zama tayi ta fuskanci Dr faduwa cikin nutsuwa da damuwa tace, Yanxu wata hudu kenan cikin yake? Abinda scanning dina yabani kenan"" dr faduwa tafada tana sake kallon takardar scanning din. Cikin tsananin damuwa sultana takalli Dr fadwa tace, Inason axubarda cikin tunda yaqi bata lafiya wuyardatake sha tayi mata yawa banason wani Abu yasameta tunda mijinta baisan dashiba. Kallonta Dr tayi cikin nazarin zancenta sbd tanaga idan anyi hakuri duk wannan wuyar zata wuce duk da itama tana tsananin tausayin rumanah din. Cikin nutsuwa tace, Inaga tunda haryakai wata hudu aqara hakuri idan yakai wata bakwai duk wannan wahalar zata rage sosai. Girgiza kai ammy tayi cikin damuwa tace, Acire kawai shine abinda nakeso yanxu. Kallonta Dr tayi cikin nazari kafin ta bude jaka ta fiddo takarda ta rubuta allura tace aje yanxu akawo zatayiwa rumanah din sai zuwa dare idan ciwon mara yataso idan tafara zuba sai akai mata ita asibiti. Cikin qanqanin lokaci ammy tasa akaje aka kawo allurar nan suka nufi dakin rumanah dake kwance tana baccin datasamu yadan dauketa. Yawu masu 'dacin damuwa da wasi wasi ammy ta hadiye cikeda tsananin tausayin rumanah dakuma takaici da baqin cikin abinda zatayi Bude ido rumanah tayi cikin wani irin laushin ciwo suna hada ido da ammy Ammyn tayi saurin sunkuyar dakanta sbd tasan haqqoqan rumanah bazasu barsuba komai daren dadewa saidai idan har zubar mata da ciki shine abinda zai kare mata ita daga masifar mineelik to ashirye take data ringa zubar mata da ciki idan tasamu. Cikin tausayawa Dr ta kalli rumanah tace, Sannu rumanah, Allura za'ai miki kisamu 'dan qarfin jiki. Murmushi qarfin hali tasaki daqyar tareda 'dan muskutawa tabada bayanta cikin nutsuwa tasoka mata allurar tayi mata tana mata sannu. Saurin barin dakin ammy tayi sbd hawayen dake qoqarin ciko idanuwanta Cikin tsananin sanyin murya takalli Dr faduwa data fito dakin tace, Awa nawa allurar zatayi kafin cikin ya lalace yafara zuba sbd........ Wani wawan jiri taji yayi mata muguwar diba tana kallon qofar palon saida Dr ta riqota tareda juyawa itama sukai ido biyu dashi tsaye yana kallonsu babu mai iya gane yanayinsa acikinsu shiya mugun tayarda hankalinsu. Manage wlh ciwon kai ke damuna yau. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *26* Haske writers association💡 *_Dan Allah daga yanxu yanzu idan kasan labari baya maka dadi zaifi idan zaka daina bi sbd wata maganar batada dadi kuma kowane marubuci idan harya fara rubuta labari to shi yasan saqon dayake son isarwa kuma idan har mai karantawa yayi hakuri ahankali zai riqa fahimatar abinda akeson isarwa dan haka pls mu riqa sanin maganar dazata fito bakinmu,_* *_Nidai nasan abinda nake rubutawa idan kasan baka iya_* *_magana mai dadiba to zaka iya tsayawa daga nan sbd bazanso kaci gaba dabiba dan abinda zaizo agaba._* Not edited. Ammy ya qureda idanuwansa dasuka mugun qara sanyata damuwar abinda tayi muryarta na rawa takira sunansa daqyar. Ya lumshe idanuwansa yasake kallonta Dr faduwa na ganin haka ta sulale ta fice dan ita ko kallo bata ishesaba. Gaban ammy yaqaraso ya tsaya cikin wani irin yanayi na tsananin 6acin rai da bata ta6a ganinsa acikiba yace, Bantaba samun tarba irin wannan ba ko sakin fuska babu bare murmushinki da murnarki. Da mamaki ta kallesa da sauri zuciyarta na qara tsinkewa dan kuwa abinda take hangowa acikin idanuwansa ta tabbarda yajisu. Murya cikin sanyi da tsananin damuwa tace, Maheer nasan kaji komai amma dan Allah inaso ka fahimci manufata tayin hakan dan nikaina ba'ason raina nayi hakan ba wlh zanfi kowa farin cikin ganin rumanah ta haifa maka 'yaya saidai I can't risk her life....... Oh please ammy karki fara kawo maganar risking life anan sbd babu Wanda ya isa yahanawa bawa shiga qaddararda Allah ya dora masa, Ammy  kinsan meyasa kuke wahala da masifar mineelik haryansu shine sbd kuna sake qarfafawa abin ne, Meye alaqar 'yayana da wannan tunanin naki dazaki min haka? Meyasa zaki rabani da abinda ko hannuna bai shigaba? Shin ammy ina iliminki da saninki yayi dazakiyi tunanin namiji zata haifa bayan bakida masaniyar hakan...... Cikin 'daga murya da takaicin abunda ke faruwa ayanxun tace, Kana tunanin ina nuna kamar nasan zata haifi namijine shiyasa nayi hakan? Amatsayina na uwa nayi hakan sbd sanin matsayin dazata hau idan ta haifi namiji Wanda kasan mezata zama idan harta zauna wannan matsayin musamman da jinininta bai zamto na sarautaba saitafi wainda suka gabata zama baraza da abin fargaba...... Cikin tsananin baqin ciki ya katseta da cewa, Rumanah har abada bazata ta6a hawa wannan kujerarba koda ta haifi namiji koda hakan na nufin ni nakar6i mulkin zan karba ni nazama masifar...... A tsawace tace, Ka riga karasa wannan damar ta zauna throne 'din mineelik tun lokacinda kace baka karbi magajin mineelik ba dan haka ko kanaso kabaka ayanxu atarihince 'dankane yanxu yakeda cikakken ikon karbar mulkin mineelik kuma kafin ya girma mahaifiyarsace kawai takeda ikon bawa duk Wanda taga damar riqon qwaryar mulkin 'danta idan kuma taso ta itace dakanta zata....... Idan angansu kenan a mineelik 'din...yafada zuciyarsa na qarasa daukar zafi. Itama cikin zafi tace, Wannan ne baka isaba sbd labarin cikin na isa a kunnen sultan bazata qara ko kwana biyu ba'a mineelik ba dan haka zabi ya rage naka kodai acire wannan cikin kodai rumanah ta rasa rayuwarta amatsayin rumanarta...... Ayau da wanine agabana bake mahaifiyata ba da bazai sake ko minti 'daya da kansa a gangar jikinsaba, Zuciyarsa tariga tagama 'daukar wuta bazai iya cigaba da maganaba ya wuceta ya nufi dakin rumanah dake kwance lamo tanaji mararta na murda mata ahankali saidai ko wani qwaqwaran motsi bata iyayi saidai jikinta dayayi mummunan sanyi hakanan takejin maraicinta na taso mata. Qamshinsa taji yashiga hancinta ahankali ta bude idanuwanta dasukai laushi takalli qofa tagansa tsaye cikin yanayin dabata ta6a ganinsa ba ta lumshe ido sbd tasan idanuwanta ne kawai ke ganinsa sbd zuciyarta tasamu sukuni. Qarasowa yayi baice komaiba ya dauketa cak ya nufi qofa da ita ya fito ammy dake zaune palon ta rafka wani mugun tagumi cikin tsananin damuwa da zullumi ta miqe tana kallonsa yazo yatsaya gabanta cikin danne halinda yake ciki yace, Komawa zanyi idan ta sauka zankawo miki ita. Kafin tayi wata magana ya wuce yabarta da baki bude idanuwanta dasukai jajir suka ciko da qwallan damuwa ganin tun yanxu alamura na neman ca6ewa. Wani babban private hospital ya nufa da ita tun ahanya yasa akai musu booking flight koda suka isa harta fara fita hayyacinta sbd jinin daya 6alle mata sosai. Cikin gaggawa aka fara dubata dan tsaida jinin dayake suma doctors din asibitin qwararrine yashiga cikinsu dan baibari kowa yataba masa itaba, Cikin ikon Allah suka samu nasarar tsaida jinin batareda cikin ya zubeba saidai kwata kwata baza'aso taringa babban motsiba sbd anriga antaba lafiyar cikin dole saiya kwana biyu yasake qarfi. Adakin datake kwance yashiga toilet ya wanke jikinsa tareda canxa shirt sbd sosai jini ya 6atasa. Sunsamu ticket din da asuba jirgin zai tashi shiyasa yasake mata wasu injections sbd motsin daza'ai da ita Yana zaune sofa din dake dakin akai kiran asuba ya tashi yayo alwala yayi sallah yana idarwa babu bata lokaci akai rubuce rubucen daza'ai suka nufi airport cikin ambulance ko mintuna ashirin basuyi da isaba jirginsu ya 'daga. Da rana tsaka suka isa Georgia direct motar asibitinsa tazo ta daukesu suka nufi asibitin nan aka fara bata sabon treatment likitocin basu zaunaba saida suka sake tabbatarda komai is back to normal. Baibar asibitin ba saidata farka ta bude idanuwanta dasukai nauyi takallesa tareda lumshe ido sbd ba qwari ajikinta sosai. Matsowa gabanta yayi yatsaya tareda kallon cikin idonta ya riqo hannunta tareda sakar mata siririn murmushi ahankali ya furta, Hey yene konjo(my pretty) Kallonsa tayi fuskarta na bayyanarda farin cikin ganinsa dakuma sunan daya kirata dashi. Da kansa ya dagata yadauketa yakaita toilet yayi mata wanka yacanza mata kaya patients sabbi ya rasa yanda zaiyi ya daure mata gashinta dole yahaqura yabarshi asake yabata tea tasha yabata magani da sauran injection dinta kafin yayi kissing goshinta yafice. Koda ya isa gida qarfe tara na dare lokacinda suhailat tagansa bude baki tayi tana kallonsa cikeda mamakin ganin jiya yatafi amma yadawo yau bayan batasaka ran dawowarsa da wuriba. Rungumesa tayi cikin danne mamakinda tace, Hey welcome. Rungumeta yayi tareda sakin ajiyar zuciya da 6oyayyan numfashi sbd shikadai yasan halinda zuciyarsa ke ciki ayanxu sbd tabbas yasan akwai rigima agaba saidai bazai ta6a bari rumanah ta Shiga abinda kakannin kakanninsa suka aikatoba koda hakan na nufin shi yafadawa abinda yayi gudu tun qurciyarsa matuqar hakan shine zai kare rumanah da abinda zata Haifa so be it. Bedroom dinsa suka nufa ya tube yashiga wanka itakuma ta nufi kicin tacewa Carolina ayi abincinda akasan maheer din naci. Daga haka takoma dakinsu amah tasanardasu dadynsu sundawo suka fito da tsallen murnarsu. Sakin fuska da jiki yayi sosai dan gudun shiga haqqin suhailat 'din da yaransa saidai cikin zuciyarsa damuwace mai tarin yawa duk da kasancewar cikin ya tsaya damuwa batabar zuciyarsaba musamman dayasan dole zasu koma mineelik sbd ammynsa takoma 'dakinta badan hakaba bayajin rumanah zata koma mineelik. Sosai suhailat ta lurada akwai abinda yake ransa na damuwa duk da abune mai wuya ka iya gane yanayinsa. Batason tana shiga abinda bai shafetaba musamman yanxu dayakeda wata matar kuma 'yar 'dakin ammynsa dan haka shishigi kan abinda babu ruwanta ba nata bane sbd kartajiyo abinda zai sakata damuwa. Fruits kawai yaci koda suka zauna dining kuma harsuka gama bai yiwa kowa maganaba duk da ko yaransa sunsaba da miskilancin daddyn nasu sbd kosu wani lokacin idan abin ya motsa baya iya yimusu doguwar magana saidai idanuwansa dake ladaftar da mutum. Da daddare koda yakira wayar Dr olie yasanar masada tasamu bacci tundazu. Kallonsa suhailat dake kwance jikinsa tayi still taqi tambayarsa meke faruwa bayan taji da hospital yake magana batai la'akari da ko ammynsa ceba dayake yasaba da haka take shiyasa bai tsaya tunanin banxa akan hakanba da haka tai bacci cikin jikinsa ya qurawa kyakkyawar fuskarta ido hakanan yakejin tausayinta sbd ba ita yakeji cikin tsakiyar zuciyarsaba, Bayajin fitar kowane numfashinsa da ita aciki saidai tanada wani irin girma da qima a idanuwansa ta yanda bazai iya barin ta quntatu akan abinda yake tsananin so ba. Rufe idanuwansa tareda dakin 6oyayyar ajiyar zuciya. Qarfe bakwai yafito wanka yakalli suhailat data shigo dakin batareda yakalletaba yana gyara gashinsa yace, Carolina ta hada breakfast na mutum 'daya a basket and it should be something light. Kallonsa tayi tana zaunawa gefen gadonsa tace, Ok amma pls who is the patient? Batareda yabar abinda yakeyiba yace, 'Yar ammy. Da mamaki ta kallesa tace, Bansan waye haka ba. Then kibarshi idan anyi discharging nata zaki ganta. Miqewa tayi tazo gabansa ta tsaya tana kallonsa yana saka rigarsa tace, Ok zanbika muje tare nadubata ko waye tunda hanyar zuwa office dina ne. Baice komaiba yagama shirinsa suka sauko tana maqale da hannunsa. Da gudu su amah dake qoqarin zama a dining sukayo gurinsa yasaki fuska cikin kulawa yayi pecking kowannensu yana cewa, Good morning to sweets angels. Good morning to you too daddy""suka fada suna kissing kumatunsa both sides. Dining suka nufa dukkaninsu sukai breakfast Shidai daqyar ya iyacin toasted bread one slice da black tea yamiqe Suma dai dayake sun gama suka dauki school bags dinsu suka fito dukkaninsu Carolina tabiyosu da basket 'dinda aka shirya breakfast dinda yace. Motarsu amah daban driver yafara wucewa kafin yashiga Lamborghini dinsa suhailat tashiga yaja suka fice daga gidan. Koda suka isa asibiti suna shiga reception yatsaya batareda yajuyo gefentaba yace, Kije room 36 zanzo idan naga dr  Andrew. Ok tace tareda kissing hannunsa ta wuce da basket din ahannnunta. Shikuma kai tsaye office dinsa ya nufa. Tana isa qofar dakin ta tsaya tareda Sauke ajiyar zuciya dukda batasa waye acikiba ta murda qofar tashiga. Zaune take tsakiyar gadon nurse na gyara mata kanta daya barbaje yana damunta. Tsayawa tayi tsakiyar dakin qafafunta na rawa gabanta yayi mummunan faduwa ganin rumanah ce, Ahankali tasauke idonta kan qaramin cikinta daya fito ga wani haske mai firgitarwa dataga tayi. Fita numfashinta yafarayi dasauri wani irin zufa ya karyo mata amma saitayi saurin kiran sunayen Allah acikin zuciyarta kafin tasauke numfashi mai sanyi tasaki murmushin qarfin hali tareda qarasowa bakin gadon inda rumanah ta tsareta da ido itama numfashinta na fita da sauri amma ganin tasaki fuska yasata qaqalo murmushi tana cewa, Sannu da zuwa. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _haske writers association💡_ *28* Not edited. Miqewa tayi tabar dining area din ta nufi dakinta tana dafe 'dan qaramin cikinta dataji yana murdawa. bayanta yabi da kallo yanajin jikinsa na qara saki sbd wata irin kewarta dake cinsa. Zame suhailat yayi daga jikinsa ya nufi stairs ya haye dakinsa. Yana shiga ko zama baiyiba yashiga wanka yafito yashirya ya kwanta tareda rufe idanuwansa sbd jin yanda zuciyarsa ke wani iri. Koda  suhailat ta shigo tagansa tayi tunanin yayi bacci tayi kissing lips dinsa ahankali kafin tafice takoma dakinta. Kwance take iduwanta arufe saidai Sam bacci yakasa daukarta data rufe idanuwanta shi take gani lokacinda ya rungume suhailat Takasa yakice abin aranta Ta jinjinawa suhailat ranar data gansu a asibiti amma bata nuna jin zafintaba bayan tasan saita fita jin zafinma. Duk yanda taso dannewa ta yakice kasawa tayi saidata saki wani irin siririn kuka tana tura kanta cikin pillow taji 'dan sauqi aranta. Qanqame pillow dinta tayi. Taji kewarsa na sake shigarsa saidai tasan yanacan da matarsa Wasu siriran hawaye suka sake gangaro mata ta rufe ido tana sakejin nauyin da zuciyarta ke mata. Acikin su uku suhailat ce kawai tasamu yin bacci cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Washe gari bai fita aiki da wuriba dan kawai yasan time dinda take fitowa daki Koda yayi wanka ya shirya cikin kayan shan iska na zaman gida palon qasan yazo ya zauna yana karanta news paper yana shan black tea. Koda suhailat taga bazai fita aiki yau Ba itama fasa zuwa tayi sbd ganin bazata iya ficewa tabarsa ba sbd gaba daya kwanakin basu sakeba sbd baida time kullum sai dare yake dawowa. Doguwar rigace mai shape sosai da budadden wuya ajikinta orange sai tayi mata kyau sosai ta qaraso inda yake zaune ta zauna kan jikinsa tana kallon fuskarsa daya 'dago idanuwansa ya zuba mata. Murmushi tasaki tareda shafo fuskarsa tana cewa, Na canzane? Maida kallonsa ga karatun dayakeyi yayi yana cewa, You're getting late for office. Sake shafo fuskarsa tayi tana murmushi tareda matso da fuskarta ga tasa sosai tayi kissing lips dinsa tace, I'm missing my husband so zan zauna tareda shi a gida yau""taqarasa fada tana hade bakinsu. Kallonta yayi itama shi take kallo tana kissing 'dinsa Sanin tunda yadawo babu abinda yashiga tsakaninsu yasa ya sake shigar da ita jikinsa yana cigaba da kissing 'dinta yana shafo wuyanta zuwa qirjinta. Jin shiru ya tabbatar mata da duk sun fice ta tashi kanta ko dankwali babu dan dama tayi wankanta,sanye takeda palazzo trouser brown da cowl neck top mara nauyi ko kadan ta fito palon tana tunanin yanda zata samu damar waya da ammy itadai gida takeso sbd zuciyarta zata iya tarwatsewa anan. Bata lura dasuba saida takusa isa daf dasu idanuwanta suka sauka kansu Gabanta yayi wata irin mummunan faduwa jiri ya 'dibeta saura kadan ta fadi yasaki suhailat dake jikinsa cikin zafin nama ya tareta ta fado jikinsa Atake ya lumshe ido tareda sakin wani muguwar 6oyayyar ajiyar zuciya. Kallonsa suhailat tayi idanuwanta nacikowa da hawaye kafin takalli rumanah din wadda tuni nata hawayen suka 6alle mata ta zame jikinta ta juya dakinta tana 'danne kukan dake taso mata Wlh batason nan tafison gurin ammy, Nan zuciyarta bugawa zatayi gwara ta tafiyarta inda bazata riqa ganinsa da matarsaba. Qofar dakinta ya qurawa ido yanaji kamar zuciyarsa zatabar qirjinsa ta shiga dakin Ko juyowa baiyiba ya nufi stairs ya haye sama sbd idan ba itace ta kusantosaba ayanxu komai na iya faruwa na 6acin rai. Zubewa suhailat tayi a gurin itama tareda sakin kukan datake riqewa ahankali, Soyayya batai mata adalciba data yiwa mijinta mugun kamun da har abada bazata samu gurbi azuciyarsa ba dan tagani tun ba ayau 'dinba soyayyarsa mai tsanani ce akan kishiyarta. Miqewa tayi tabar palon tana shiga dakinta ta toshe baki tana sake sakin wani siririn kukan. Rumanah ma kukan takeyi sosai tana dafe cikinta dake motsawa gabaki daya kewar ammy takeji. Ganin zaman gida qara hargitsa masa lissafi zaiyi ya dauki keys din mota yasauko yafice gaba 'daya. Yini guda cur kowaccensu a dakinta tayisa Carolina ce ta kaiwa rumanah abinci sbd dama tasaba kai mata kullum matuqar bata fito ci ba Wanda tsatsauran umarni ne daga maheer daya bata akan koyaushe ta tabbarda rumanah taci abinci. Suhailat bata fitoba sai maraice sosai lokacinda taji hayaniyar su amah sundawo daga Islamic classes da ake kaisu daga school kullum shiyasa sai yamma suke dawowa. Wanka tayi ta gyara fuskarta sbd idanuwanta dasuka kumbura ta sanyo dogon yellow skirt da red floral lace top ta fito tafara qoqarin sakewa cikin 'yayanta tana tambayarsu school dakuma abinda yafaru a school 'din sbd tasamu tasake daga damuwarta tun kafin yadawo yagano halinda take ciki. Itama rumanah jin hayaniyarsu a palo yasa ta tashi tayi wanka ta sako purple doguwar riga mai guntun hannu kanta sanye da hula bata shafo komaiba a fuskarta sbd tata fuskar bata kumbura ba tadaiyi jajir kasancewar tafi suhailat zama fara sosai. Idonta kawai ta sanyawa kwalli tafito. Kallo daya sukaiwa juna kowacce ta qaqalo murmushin dole suhailat tafara cewa, Hayaniyarmu ta tayar dake ko? Murmushi tayi tareda girgiza kai tace, Aa dama natashi kawai jin gidan tsit yasa nayi tunanin Baku dawoba yanxu ina jin hayaniyar nace bari nafito. Shiru sukayi kowacce na 'dan jansu amah da zance sama sama ahaka dai kuma suka maida hankalinsu ga kallon wani series da akeyi THE LEGACY a cwtv. Lokacin sallah nayi suka miqe kowa yaje dakinsa yayi sallah babu wadda tasake fitowa sai bayan sallar ishai. Kiransa suhailat tayi sbd jin kozai dawo da wuri su jirasa dinner yace su jirasa zai dawo sbd yasan dole itama rumanah zata jira. zaune suke Suna fira sama sama rumanah takalli suhailat cikin jin nauyi tace, Kozaki kiramin ammy tunda nazo ban gaishetaba. Kallon mamaki suhailat tayi mata saidai ba hurumintaneba tambayar meyasa haryanxu batada waya sai kawai ta dauki wayarta dake gefenta tayi dialing numbern ammy tamiqa mata tabar gurin data bata damar magana. Cikin kulawa ammy data daga wayar tace, Suhailat ya kuke? Cikin sanyin muryar dakeson yin kuka tace, Ammy ina wuni? Wani irin sanyi da farin ciki yasa ammy tashi zaune daga kishingiden datake tace, Rumanah ya kike? Ya jikinki? Lafiya klau ammy naji sauqi sosai, Yaya su ummee nayi kewarku ammy inason nadawo gida. Cikin kulawa ammy tace, Bakyajin dadin nan ne dakikeson kidawo bayan mijinki na tareda ke ga suhailat nasan itama batada matsala. Ina jin dadin nan din amma nafison nadawo gurinki. Shiru ammy tayi cikin nazarin zancenta sbd tasan yanayi na zaman kishi dole wata rana akwai jin zafi amma dole zatai hkr sbd shine auren. Murmushi mai sauti ammy tasaki tace, Qiyi hkr rumanah kibari idan kin kusa haihuwa saiki dawo amma idan kinji bazaki iyaba kifadawa maheer din yabari kidawo gida idan kin haihu saiki koma daga baya. Shiru tayi sbd batasan yazata fada masaba bayan qilama ya manta da ita kwata kwata ta matarsa yakeyi dama ita sbd ciki aka aureta yanxu tunda tasamu shikenan aikinta ya qare. Hawaye suka gangaro mata murya na rawa tace, To ammy. Tambayarta ammy tafarayi akan lafiyarta da lafiyar cikinta daqyar take iya amsawa sbd nauyi da damuwar datake ciki. Tana gama wayar koda ta 'dago yana tsaye bakin qofar palon yana jifanta da wani irin kallo dayasa jikinta rawa tana hango tahowar suhailat ta miqe ta nufeta ta miqa mata wayar cikin sanyin murya ta nufi dakinta suhailat data hangi irin kallonda yake biyo rumanah din dashi ta hadiye abinda takeji tace, Kitsaya kiyi serving dinsa dinner zanyi making wani call ne. Tana fada ta juya takoma dakinta tareda saurin dannawa qawarta siyah kira sbd 'daukewa kanta damuwa. Tana shigewa daki shima ko kallon inda rumanah din take baisake yiba ya nufi dakinsa ransa na 6aci da yanda rumanah kamar gudunsa take dakuma yanayin daya hango atareda suhailat. Wanka yayi ya shirya cikin kayan bacci farare as usual kafin ya dauki wayarsa yakira suhailat amma number busy har kusan tsawon mintuna Dior Slippers yazuro tareda saukowa qasa ya nufi bedroom dinta yana kawowa palo yaganta tsaye bakin qofar bedroom din rumanah tayi knocking. Tsayawa yayi yana kallonta lokacinda rumanah ta bude mata fuskarta daukeda murmushi tace, Kina neman wani abune? Kishigo. Aa basai nashigoba dama baby baici dinner bane shine nace kozaki diba kikai masa kaina yana ciwo banaso nayi kaida kawo da yawa gashi gobe dole naje office tunda banje yauba. Sauke kai tayi tana ta6a yatsan hannunta cikin sanyi tace, Dan Allah kiyi hakuri amma bazan iya zuwaba ni tamkar baquwace anan dan haka banajin zuwana yanada wani mahimmanci zan diba nabawa Carolina takai masa. Da mamaki suhailat takalleta idan ta fahimta daidai saitakejin yanayin maganar rumanah din kamar batason zuwa gurinsane sbd wani dalilin bawai dan tana matsayin baquwaba kamar yanda tace. Bazata iya tsayawa takurataba dama sbd fita haqqin su biyun ne yasa tace taje dan haka babu wata damuwa tace, Shikenan kibawa Carolina din takai masa. Ta juyawarta tabar gurin itama rumanah dakinta takoma ta kwanta. Juyawa yayi dakinsa yana zuwa ya zauna ransa amasifar 6ace. Kiran suhailat ne yashigo wayarsa da farko bai dagaba saidata sake kira ya daga Cikin kulawa tace, Sorry baby I......bata qarasaba yace, I need a coffee. Ajiyar zuciya tasaki kafin tace, Ok. Kitchen taje tasaka Carolina ta 'dora mata tana gamawa ta zubo masa a coffee cup ta nufi dakinsa. Tana shiga taqarasa jikinsa ta zauna tareda miqa masa yakarba yafara sha yana duba saqo a wayarsa koda yagama yamiqa mata cup din ta ajiye kan table yace, Ruwa. Tashi tayi taje ta dauko masa yasha ta karba ta ajiye tareda komawa jikinsa tana cewa, Baby are you ok?I mean you......jawota jikinsa yayi ya rungume tareda sakin ajiyar zuciya sbd jin 6acin ransa ya ragu sbd 'yar kulawar data nuna masa. Murmushin jin dadi tasaki tana cewa, Ok ok I got it,you're missing me right? Wani irin murmushi yasakar mata sbd girma da ko yaushe take qarawa a idanuwansa dan yasan tana fadane dan tabawa kanta matsayi dakanta idanma bai bataba sbd ta cirewa kanta damuwa bayan shi yana iya hango damuwar a idanuwanta. 'Daga kai yayi tareda matso da fuskarta tasa yana goga hancinsu yace, I always missed this sweet voice of mrs m.a shams idan bata kusa. Dariyar jin dadi tayi soyayyarsa naqara shigarta ya hade bakinsu yana zura hannunsa cikin rigarta ta riqe hannun tana daria tace, Heyy kana sakani waiwayi plsss. Daka tawa yayi yana kallonta Tayi dariya tareda maida bakinta kan nasa ba musu yasake matseta jikinsa yana shafata daganan ya dauketa suka koma kan gado. Kasa bacci tayi sbd tunanin baici abincinba ta tashi zaune tareda saukowa gadon ta nufi qofa ta fita taje dining ta dauki abincin datasan dominsa akayi taje kitchen tayi warming dinsa kafin ta jero a tray tareda komawa daki ta canxa riga zuwa doguwar riga mara hannu da wani sahirtattan qamshi ta dauka ta nufi saman. Kai tsaye ta bude qofar palon tashiga ta nufi qofar bedroom dinsa tayi knocking ahankali. Shiru babu alamar za'a bude tasake knocking lokacin suhailat ta taso daqyar daureda towel dinsa sbd bazata iya mayarda kayanta batai wankaba. Cikin muryar gajiya tace, Carolina is that you? Muguwar faduwa gaban rumanah yayi Tray din hannunta yafara rawa tayi saurin ajewa kan table din palon ta juya salin alin tabaro saman tadawo dakinta Tana zuwa ta kwanta tana adduar bacci sbd sotake yayi gaggawar daukarta batareda zuciyarta tasamu damar wani wahalallen tunani ba. Ita kuwa suhailat najin shiru jikinta yabata rumanah ce takasa budewa ta juya sbd babu dadi tabude mata qofa a wannan yanayin datake ciki. #mamuhgee #vote and follow pls. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *27* Aje basket din hannunta tayi tana sake qaqalo murmushi tace, Ashe kece babu lafiya baby baifadaminba kawai yafadamin numbern dakin ne, Sannu ya jiki? 'Daga kai tayi ahankali tana cewa, Alhmdllh. Shiru dukkaninsu sukayi babu wacce numfashinta bai fita da sauri sbd ganin 'yar uwarta. Suhailat cikin jikin rumanah din take satar kallo dan kuwa batasan haka take kishin mijintaba saidataga cikin dan kuwa Allah ne kadai yasan irin ciwo da radadin datakeji axuciyarta saidai tana qoqarin fincikewa sbd batason zubarwa da kanta qima a gurin mijinta da 'yayanta harma da rumanar datake kishiyarta. Rumanah kuwa jitayi duk atakure take da wanzuwar suhailat din gashi nurse tagama abinda takeyi ta fice. Hakanan takejin bata iya kallonta sosai sbd ganin take zuciyarta da shaidan zasu hasaso mata maheer atareda suhailat din Wanda hakan na matuqar girgiza zuciyarta. Cikin kulawa suhailat ta miqe ta bude basket din ta hada mata black honey tea sai pancakes da toasted chicken datai laushi sosai ta zuba matasu a plate tareda aje matasu yanda zata iya ci. Cikin sanyin murya rumanah tace, Nagode amma inaso zanshiga toilet.... Wayar suhailat dince tayi ringing ta sauka da sauri sbd mum 'dintace batareda taji mai rumanah din ke fadaba ta fita dan amsa wayar. Ganin ta fita yasa rumanah sauke qafafunta qasa ahankali ta sauko ta nufi toilet din dake dakin ahankali sbd jiri. Tana kaiwa tsakiyar dakin wani irin jiri ya dibeta daidai shigowarsa dakin. Saida tajita jikinsa tayi saurin sakin ajiyar zuciya sbd ta sadaqarda cikinta yagama zubewa idan ta fadi. Bude idanuwanta data rintse tayi takallesa cikin fargaba sbd ganin kallon dayake mata murya na rawa tace, Toilet zanshiga. Yanda ya dauke gira daya yasa tasan menene azuciyarsa tayi qasa dakai cikin tsananin sanyin murya tace, Yi hakuri bansan zan..... Just shut up"""yafada yana daukarta gaba 'daya ya bude toilet din suka shige. Sauketa yayi ahankali kamar kwai Ta dago takalli fuskarsa taga ba wasa tasaki 6oyayyan murmushi cikin zuciyarta tana cewa, Ko fushi kyau yake masa. Brush ya miqa mata ta karba tayi tana kallonsa sbd kallonsa yanxu matuqar nishadi da nutsuwa yake bata tana gamawa ya miqa mata towel tareda jawota jikinsa yazare mata kayan jikinta itadai ido kawai take binsa dashi sbd yau ko ta6insa nutsuwa yake bata. Da yake shower ce bai shigaba ita kadai tashiga tayi wankan shikuma yana tsaye gaban mirror yana goge inda rigarsa ta baci da ruwan allurar dayaje yiwa wani patient kafin yashigo dakin. Tana gama wankan ta dauki towel ta daura tareda zare shower cap din kanta ta tsaya gaban madubin da yake dubawa tana fuskantarsa. Wasu kayan yasanya mata saidai bada bra ba duk saiyaji ransa yabaci da yanda kayan patients din sukai mata kyau amma bai nunaba yasake gyara mata gashinta ya dauketa suka fito tana kallonsa gira 'daya ya dauke yace, Wannan kallon fa matata tana nan so be carefull bata hadani da komaiba. Murmushi daya bayyana fararen haqoranta tasaki tareda sake qanqamesa tana fitarda sautin murmushinta ahankali shima murmushin gefen baki yasaki suna kawowa tsakiyar dakin sukai ido hudu da suhailat dake zaune tayi musu kallo 'daya ta dauke kai tana qoqarin danna kira awayarta. Saurin saukowa jikinsa rumanah tayi sbd taji nauyin suhailat din sosai koba komai ka girmama mai girmama kansa ta zauna bakin gado tana suuke kanta qasa. Kallo 'daya yayiwa suhailat yagano halinda take ciki yaji tabasa mugun tausayi sbd baisan lokacinda ta dauka azauneba gashi sun dade aciki gashi qila batasan yana cikiba. Hannu yakai yakamo hannunta tareda miqar da ita ya matsota gabansa yana kallon cikin idonta datake qoqarin 6oye halinda take ciki cikin kulawa yace, Are you ok? Kai ta 'daga masa batareda yakallesaba Yayi kissing forehead dinta yace, I will be in my office""yasa kai yafice yabarsu. Jawo abincin rumanah tayi tafara ci hannunta na rawa sbd rawar da zuciyarta keyi. Suhailat ma batareda takalli fuskar rumanah din ba tace, Zantafi office am getting late Allah yasauwaqa. Tana gama fada ta dauki handbag dinta ta fice hawayen datake riqewa suka gangaro mata ko office dinsa bata biyaba ta wucewarta saidata isa office dinta ta rufe siririn kuka ya balle mata amma dannesa tashigayi sbd bataga dalilin kukanba tunda dama tasan tanada kishiya meye abin jin zafi dan taganta da ciki bayan itama Allah yabata nata 'yayan ba juya yayitaba. Saidata samu nutsuwa tayi masa text tace ta wuce office and she's very late so shiyasa bata biyo office dinsaba. Tana ficewa rumanah ta aje breakfast din sbd dama turawa kawai takeyi. Yana gama karanta text dinta ya aje wayar tareda lumshe fararen oily eyes dinsa. Yinin ranar dukkaninsu a darare sukayisa sbd kowanne da abinda ya maqalewa zuciyarsa. Baibar asibitin ba yau sai qarfe goma na dare lokacinda rumanah tayi bacci kenan. Koda yakoma gida suhailat bata nuna damuwar komaiba a fuskarta itada 'yayanta su maqalqalesa suna masa oyoyo Yayo wanka bai sauko cin abinciba sbd yaci pizza tareda rumanah a asibiti. Koda suhailat taji cewar yayi dinner murmushi kawai tayi tace, Ok bari nacewa Carolina tasaka a fridge. Kodata dawo dakin yana kwance wayarsa a kunnensa yana magana da antynsa wadda yake biwa tana qara basa haquri akan abinda yafaru shidai kunnuwane kawai nasa baya iya zuba dogon zance. Kwantawa tayi ajikinsa tareda rungumesa ta rufe ido alamar bacci Yayi mamaki sbd basu cika kwana daki dayaba koman dare wani lokacin dakinta take komawa ta kwana. Koda yagama wayar tayi bacci yakalli fuskarta kafin ya lumshe idanuwa fuskar rumanah daya baro tana barci tafado masa yasake rungume suhailat ajikinsa yana kamar rumanah ce ajikin nasa. Washe gari ma tare sukaje asibitin saidai ko zama batayiba gaisawa kawai sukayi ta wuce gurin aikinta sbd ganin irin kallon da maheer kewa rumanah sbd sai yanxu cikinta yafito dakyau sbd kayan da aka canxa mata sunso kamata saikuma basu kama 'dinba. Bayan wucewar suhailat nurse 'din dake kula da ita ta fita sbd idan yashigo fita sukeyi. Kallon 'dan cikinta yayi batareda ya amsa gaisuwartaba ya dauki file dinta yafara dubawa. Qamshinsa daya cika dakin ta shaqa tana lumshe ido cikeda qaunarsa mai zafi dake cin zuciyarta. Yana gama dubawa ya kalleta a miskilance yace, Did you bleed today? Girgiza masa kai tayi kala kallonsa ya juya yafice baisake cewa komaiba. Numfashi tasauke a sanyaye ta zame takwanta. Kwananta biyar a asibitin akayi discharging dinta tunda suka kamo hanyar gida numfashinta ke fita da qarfi Jin tayi tafison komawa Libya gurin ammy hankalinta zaifi kwanciya acan. Suhailat ma tunda tasan zasu dawo gida anyi discharging dinta jikinta yake sanyaye. Carolina tagyarawa rumanah dakinta tun na farko sosai. Qarfe goma sha biyu suka iso tareda driver sbd shi theatre zaishiga. Koda suka iso gidan tuni kayanta dayayi shopping online suka iso har ankai mata dakinta Itadai suhailat tana bedroom dinta sbd ita bata iya munafurciba arayuwarta bazata iya tsayawa tana rawar jiki akan abinda tasan ba haka bane cikin zuciyarta, Abinda tasani shine bazata qi rumanah ba bakuma zatai munafurcin nuna mata soyayyar qaryaba saidai zata mutumta ba sbd mijintane ya ajiyeta kuma as along as babu Wanda ya wulaqanta wani acikinsu to zasu zauna lafiya babu takura saidai batai alqawarin ringa zaunawa suna fira tareba gwaradai nesa nesa da juna saisunfi mutunta junansu. Carolina ta tarbota daga mota suhailat na dakinta suka shigo kai tsaye daki rumanah ta nufa ta zauna bakin gado tareda sakin ajiyar zuciya ahankali. Ta jima a zaune kafin tamiqe tashiga toilet tayo wanka tazo tasaka doguwar riga mara dogon hannu ta daure gashinta ta saka qaramar hula mara nauyi tayi sallar ishai da akai tana gurin wanka tana idarwa ta fito palo tana qoqarin sakin fuskarta ta nufi kicin inda tajiyo muryar suhailat tana waya taje daukar Abu a fridge. Gama wayar suhailat tayi ta juyo tana Murmushi tace, Patient ya jikin? Barka da dawowa gida. Jiki alhmdllh naji sauqi sosai Ina su amah banji hayaniyarsuba gashi naga lokacin dawowarsu daga school haryayi nisa da wucewa. Sundawo tun dazu suna study room sbd Anfara musu exams. Jinjina kai tayi tareda ficewa tabar kicin din Itama suhailat tana gama abinda takeyi ta fice. Yini guda adaki tayi abinta ko abinci ma daki Carolina ke kai mata. Ita kuwa suhailat abinda ke gabanta kawai takeyi ba damuwar komai. Baidawo gidanba sai cikin dare lokacin kowa gidan yayi bacci sama ya nufa dakinsa kai tsaye yashiga yayi wanka harya gama shirin kwanciya ya kwanta babu suhailat bare rumanah da dama baisa ran zata iya zuwaba. Washe gari koda yayi shirin office harya wuce rumanah na dakinta bata fitoba saida dukkaninsu ta tabbatarda suntafi gurin aiki ta fito. A dining ta yi breakfast dinta ita kadai tana gamawa tadawo palo ta zauna tana kallo duk da hankalinta ba akan kallon yakeba duka. Ahaka dai ta wuni ita kadai sai Carolina dake dan tayata fira sama sama sbd ba laifi Carolina din tafi sakewa da ita akan suhailat sbd tafi sake mata. Suhailat ce tafara dawowa da yamma lokacin tana palon zaune tana gyaran farcenta sanyeda blue skinny jean da red loose top sai gashinta dake dunqule cikin hula red cikin sakewar fuska sosai tayi mata sannu da zuwa. Cikin sakewa itama ta amsa tana cewa, Duk kadaici ya dameki babu kowa sai Carolina kuma ita bawani sakewane da itaba. Nikuma naji dadin kasancewa da ita sbd ba laifi muna sakewa da juna sosai. Dakinta ta nufa tayi wanka ta sanyo white skinny jean da white chiffon shirt tareda black hula ta fito palon ta zauna kusada rumanah tana cin pancakes suna kallo. Sallar magrib tasa rumanah barin palon ta nufi dakinta. Sallah tayi magrib tayi bata fitoba saida tayi sallar ishai ta shiga wanka tana fitowar Carolina tayi knocking ta sanarda ita ana jiranta suci dinner. Straight skirt tasaka black da black d&g shirt hasken fatarta yafito sosai cikin black shigar ta dauro siririn black scarf tafito tana fidda siririn qamshi ga cikinta daya fito cikin kayan sosai. Tana fitowa kallo daya suhailat tayi mata ta dauke kai tana murmushi tace, Ok everybody time for dinner. Suka miqe fammah na maqale da hannun rumanah suka nufi dining suka zauna. Abinci sukeci cikin nutsuwa itadai dama tafadawa Carolina noodles With veg zataci saigashi bata wani ci sosaiba saima papaya drink datake ta sha. Coat dinsa riqe ahannu yashigo palon yana waya. Kallo daya yayiwa dining area 'din yaji gajiyar daya 'debo ta ninku., Da gudu suhailat ta taso ta rungumesa tareda basa peck tana cewa, Welcome baby. Rungumeta yayi shima yana kallon idon rumanah datai saurin 'dauke ido akansu jikinta na rawa. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *30* *_ita soyayya da fahimtar juna Allah ne yake sakata acikin zukatan wainda yaso kuma babu wani shedani daya isa ya raba abinda Allah ya hada sbd shi daya hada yasan abinda yasa yahada dan haka soyayya da qaunar dake tsakanina da daughter na BILLYN ABDUL babu wani shedani ko munafukin daya isa yashiga tsakani bare yaraba_* *_Wasu sunso hada fitinar cewa labarinmu yazo 'daya to ai dama dole labarinmu zaiyi kamanceceniya sbd ra'ayinmu 'daya shawararmu 'daya abinda yake gudana aranmu 'daya to mezai hana labaranmu kamanceceniya?_* _*Naso dakatawa sbd wasu dalilai saidai hakan na nufin mundakata gaba 'daya daga TARAYYA har RAINA KAMA sai munafukan dake cewa 'dayane su qarasa labarin tunda dayane ai bazai musu wuyaba saidai kuma masoyi duk inda yake yafi maqiyi shiyasa muka bar komai ya wuce kuma kuji da babbar murya duk munsanku masu halayen kafiran farko*_ _*MAMUH DA BILLYN ABDUL BAZAKU TA6A GANINSU YANDA KUKESOBA*_ _*Tarayya daga yanzu har gamawarsa sadaukarwane ga daughter na BILLYN ABDUL*_💋 _*Z B I i love you guys as much*_💋 _sorry wainda ban daga wayarsuba da kuma basu reply na massage dinsu_ _naga masoya nakuma gode_🤝 Not edited. Ammy na gama waya da maheer din jikinta yayi sanyi matuqa sbd Dama tasan hakan na zuwa sbd tun barowarsu mineelik tasan sultan yazuba tsaro sosai akansu ta yanda duk wani motsinsu arayuwarsu yana sane dashi saidai batai tunanin zai nemesu da wuri hakaba. Shikuwa lokacinda saqon ya Isar masa yana hospital kallo 'daya yayiwa abaas dameer aqeel da sultan ya Aiko takanas daga mineelik din ya dauke kai tareda 'daga masa kai alamar yaji yabasa guri, Rufe ido yayi tareda jan 6oyayyan numfashi. Da wuri yadawo gidan koda yashigo rumanah ce kawai a gidan tana dakinta kwance tana bacci sbd kwanakin Sam bata cika lafiya ba sbd girma da nauyin cikinta. harya taka steps biyu na zuwa dakinsa ya tsaya cak tareda juyowa yakalli qofar bedroom dinta, Yau gaba 'daya baiganta ba sbd suhailat ce keda kwanan kuma tunda safe yafito shiyasa gabaki daya yau ya rasa gane kansa ga qarin saqon sultan daya riskesa. Juyowa yayi yadawo ya nufi dakinta batareda yayi knocking ba yashiga tareda turo qofar. Kallonta yayi yanda ta tayi kwanciyar tana dafe da cikinta da alama hannunta nakan cikin tayi baccin. Sanyin ac dayayiwa dakin yawa yakalla tareda qarasawa yadauki remote yarage ac din. Bakin gadon yazauna tareda zuba mata ido tsawon lokaci ya lumshe ido yabude ahankali yanajin wani irin yanayi mai zafi game da ita. Riqo hannunta yayi ya matse cikin nasa ya rufe ido yana qoqarin yakice fargabar datake shigarsa akanta,. Ahankali ta bude idanuwanta ta zuba a fuskarsa tana masa kallon mamaki sbd baitaba shigowa dakinba a iya sanintama baya shiga dakunansu. Qoqarin tashi tafarayi ya mayar da ita tareda girgiza mata kai ahankali still yana kallonta. Mamakine yasake kamata ganin yanda yake kallonta cikin wani yanayi., Ahankali ta furta, Dehina neh?(are you ok?) Lumshe ido yayi tareda 'daga mata kai. Cikeda wani sabon mamakin takallesa sbd ganin ya amsa mata ba kamar yanda yasaba zuba maka ido ko shareka idan ka tambayesaba. Kasa 6oye mamakinta tayi hakan yasashi sakin Murmushi yana sake damqe hannunta dake cikin nasa murya a shaqe yace, Kinshirya ganin ammynki? Saidata kalli cikin idonsa tasaki murmushin kwanciyar hankali ta daga kai. kinason komawa mineelik? Ba zato taji tambayar takallesa gabanta na faduwa takasa cewa komai. Kwantawa yayi jikinta zuciyarsa na qara shiga wasi wasin kaita haihuwa mineelik. Kallon fuskarsa tayi taga idanuwansa a rufe tasan baya buqatar hayaniya alokacin Sai kawai tayi shiru tareda lumshe nata idanunwan tareda sake riqe hannunsa dake cikin nata itama. Sun jima ahaka har bacci yadaukesa itadai kasa baccin tayi ta zuba masa ido hankalinta yaqi kwanciya Sam da yanayin data lura yanaciki. Maida tunaninta ga maganarsa ta zuwa mineelik dayace tayi taji gabanta yayi mugun faduwa, Tabbas tasan zata koma mineelik haihuwa saidai duk lokacinda ta tuno hakan hankalinta na matuqar tashi sbd jikinta na bata idan takoma shikenan ta rasa maheer, Maheer yazamo wani babban 6angare na rayuwarta, Yazamo zuciyarta datakejin bazata iya rayuwa babusaba, Shine uban abinda zata Haifa saidai tanajin kamar tafison kasancewa da maheer din akan abinda zata Haifa dan idan ta tuno abinda ke cikinta mineelik da zagayenta suke jira ta haifo aga ko menene ke qara bata tsoro da daga mata hankali. Baccin baiwani dadeba ya farka kansa na 'dan ciwo ya kalleta da sauran bacci a idanuwansa yace, Ki daukomin kaya zanyi wanka anan. Saukowa gadon tayi ta nufi qofa yabita da kallon tausayinta da qaunarta mai qarfi sbd ganin girman cikinta cikin laushin murya qasa qasa yace, Hey. Tsayawa tayi tareda juyowa ya tashi zaune tareda lumshe ido ya miqa mata hannu ahankali. Jitayi zuciyrta tasake sanyi ta dawo ahankali ta kama hannunsa ta zauna gefensa sukayi shiru dukkansu sai can yasaki ajiyar zuciya ahankali yana dago da fuskarta suka kalli juna ya shago cikinta cikin wani irin yanayi yace, Allah ya albarkaci zuriata. Dora hannunta tayi kan nasa cikin sanyin murya ta furta amin. Tashi yayi yakama hannunta cikin kulawa suka nufi toilet yayi wanka yayo mata, Sosai yake cikin wani irin tunanin yanda zaiyi nisa da ita idan suka koma mineelik sbd har cikin zuciyarsa yakejin duk wani laulayin cikin datake ciki. Suna fitowa da kansa ya bude wardrobe ya dauko mata doguwar rigar chiffon mara nauyi yasaka mata,tasaki murmushi tana kallonsa ta madubi yanda yake gyara kansa. Tsayawa yayi yana kallon Murmushinta qasa qasa yace, I'm all yours zaki iyayin abinda yafi kallonma. Zaro ido tayi cikin wata muguwar kunya ta miqe da sauri zata bar gurin yadawo da ita tareda Rungumeta ta baya jikinsa da babu kaya ya hadu da bayanta da kusan rabi yake abude sbd yanayin rigar. Shinshina gashinta yayi tareda lumshe ido yana sake matseta jikinsa sbd tuni tasakar masa da sabuwar kasala bakinsa yakai kunnenta cikin kasala yace, Meyasa zakiji kunya bayan kinsan yes you have all the rights kiyi abinda yafi kallon. Qanqamesa tayi cikin wata sabuwar kunyar tace, Please kabari. Ba musu yayi shiru yana murmushi tareda mayarda hannunsa kan cikinta ya lumshe ido ya bude, Allah ne kawai yasan irin son dayakewa cikin jikinta sbd ganinta daukeda cikinsa ke sakar masa nutsuwa da wani irin farin ciki sbd ganin ita 'din dai tasace mallakarsa,gonarsa,hurumsa da babu Wanda ya isa tunkarowa duk fadin duniya, Gonarsa da babu Wanda ya isa yayiwa kallo biyu batareda yasa anraba kansa da gangar jikinsaba, Allah ya 'dora masa son amah fiyeda dukkanin sauran 'yayansa da abinda ya mallaka kuma bayajin zai samu wani 'da ko 'yar dazaiso kamar amah 'dinsa sbd tsananin soyayyar yarinyar ajinansa take tun ranarda aka haifi har zuwa yanzu, Abinda ke cikin rumanah kuwa tun 'yanxu yanajinsa cikin azuciyarsa sbd shine abinda yake nunawa duniya gabaki 'daya rumanah tasace shikadai shiyasa yake tsananin qaunar cikin tunkafin yazo duniya. Fuskarsa ta shafo tana Murmushi tace, Kana tunanin mezan Haifa ne? Kallonta yayi yakalli cikin ya riqo hannunta cikin nasa cikin yanayi na sanyin murya yace, Bana tunanin mezaki Haifa ta 6angaren jinsi sbd agurina ko me zaki haifa shine babban abinda zai cigaba da sakani farin ciki har abada sbd shine fitilarda take haskomin abu mafi soyuwa azuciyata. Sanyi jikinta yayi takallesa da idanuwanta dasuka ciko da hawaye tasake riqe hannunsa cikin sanyin murya tace, Ko agurin haihuwarsa na mutu ayanzu nasan bazaiyi maraici kamar niba, Abinda yake cikina shine hasken rayuwata sbd shine cikakkiyar shaidar soyayyata da batada mahadi, Shine abu mafi soyuwa a zuciya da rayuwata sbd shi tsotsonkane saidai bansaniba ko zan cigaba da zama uwa agaresa kamar yanda nake mafarki..... Rufe mata baki yayi yana kallon idonta yace, Har abada kece zaki zauna amatsayinki na mahaifiyarsa babu Wanda zai rabaki da abinda zaki Haifa.... Mutuwa ko qaddara "" tafada muryarta na rawa sbd tsoro da fargabar dake shigarta. Girgiza mata kai yayi da sauri tareda Rungumeta cikin wani irin yanayi daya bata mamaki yace, Ina roqon Allah daya cigaba da azurtani da 'yaya mata daga dukkanin matana. Ajiyar zuciya ta sauke ahankali ta furta amin saidai hankalinta yariga yatashi sbd ganin shima bayason ta haifi namijin sbd guje mata arabata da 'danta da mijinta. Shiru sukayi tsawon mintuna saida suka samu nutsuwa kafin yatashi suka fito ya nufi dakinsa ya shiryo yana saukowa suhailat tashigo agajiye sbd cikinta dayayi girma itama. Cikeda tausayinta ya ware mata hannu ta rungumesa yayi kissing goshinta batareda yace komaiba. Cikin kulawa tace masa, Thank you baby"" sbd tasan sannu yake mata da gajiyar dayaga ta debo koda baiyi maganar ba. 'Dauke kai rumanah tayi tareda juyowa ta nufi cikin ahankali zuciyarta na bugawa da sauri sauri. Bayanta yabi da kallo jikinsa na sanyi Ganin yanda yayi yasa suhailat juyawa taga rumanah ce harta kusa shigewa kicin Ta juyo takalli idanuwansa taga yanda yanxu soyayyar rumanah bata 6oyuwa acikinsu duk kuwa da iya qoqarinda yakeyi dan boyewar amma soyayyarta tafaracin qarfinsa sai kawai taji yabata tausayi tasaki murmushi qarfin hali ta dafasa cikin sanyi tace, I will go and freshen up. Tana fada ta wuce idanuwanta na cikowa da hawayen tausayin kanta da rayuwarta nan gaba sbd. Ya lurada halinda itama tashiga yabi bayanta da kallo tausayinta nasake kama zuciyarsa ya zauna sofa yana sake kallon qofar kicin cikin damuwa. Da daddare gurin dinner kowa nacin abinci cikin nutsuwa da rashin sukunin zuciya ya 'dago ya kalli rumanah dake cin fruits kawai yaji damuwar hakan sbd batason cin abinci saiya sakata dole idan suna sukadai kenan sbd lurada hakan yasa wani lokacin suhailat ke qin cin abinci a dining taredasu sbd su sake saitace akai mata daki. Bayan sungama harzai bar dining din yacewa Carolina data qaro drink taje ta dafo masa noodles kadan a plate. Suhailat najin haka tasaki murmushi tace, Ok baby nizanje na kwanta bacci nakeji sosai so gud night. Riqo hannunta yayi yana kallonta yace, Zamu koma mineelik this weekend so idan kinje office kiyi magana dasu. Ok tace gabanta na faduwa akaro na farko taji ankirama sunan mineelik hankalinta yatashi bare dataji zasu, asanyaye ta nufi dakinta tashige dama yau take fita girki. Kallon qofar dakin rumanah yayi yanufa yashige lokacin harta gama shirin bacci. Da mamaki takallesa ya qaraso bakin gadon ya hau ya kwanta yana lumshe ido. Ranar asabar suka wuce Libya dukkaninsu sbd lahadi zasu isa mineelik gashi lokacin cikin rumanah yashiga wata na takwas suhailat kuma wata shida kuma sosai yake bata matsala sbd cs dinta shiru kawai tayi sbd batason dagawa maheer hankali saidai Sam batajin wannan karon cikin nada lafiya kamar sauran cikin datai tayi nasu amah. Lokacinda ammy tayi ido biyu da rumanah da cikinta jin tayi hawayen farin ciki sun ciko idanuwanta sbd Allah ne kawai yasan iya adadin qaunar datakewa rumanah gashi tana 'daukeda cikin maheer 'dinta datafi kaf cikin 'yayanta. Rungumeta tayi cikeda farin cikinta daya kasa 6oyuwa Rumanah ma batasan haka tayi kewar ammynba saidata ganta hawaye suka ciko idanuwanta ta rungume ammyn tana cewa, Ammy nayi kewarki sosai. Cikin farin ciki sosai ammy ta zaunar da ita tana cewa, Rumanah babu ranarda ammynki bata kewar kulawar dakike bata. Murmushi tayi tace, To ammy aigashi nadawo. Kallon maheer daya shigo lokacin tayi tace, Ko kindawo babu ruwan ammy dasaka matar mutane aiki bayan ga yanayinda ma take ciki. Yagane ammy dashi take yayi kamarma baijiba ya qaraso gurinta suka rungume juna yace, Nafekushy ya Ammy. I miss you too maheer""tafada tana sakinsa takamo hannun suhailat dake tsaye bayansa tana Murmushi ahankali Tace, Suhailat yakuke?da yaran duka. Lafiya klau ammy munsameku lfy? Alhmdllh zoki zauna suhailat kinji sannunki. Zama sukayi rumanah kuwa sashen s salma ta nufa acan s salma ba qaramin farin cikin ganin rumanah tayiba harda tsokanarta tayi da cewa, Yanzu bada dadewaba zansa akira aarib yazo dalibarsa tadawo. 'Yar qaramar dariya tayi tace, Idan yazoma babu ruwanah da abinda zai samesa. Dariya s salma tayi tace, Eh mana tunda miskilin mijinki nanan dole zakice haka. Tsayawa yayi bakin qofar yana kallon yanda tasake take magana sosai da s salma baitaba ganin tayi surutu sosai hakaba musammanma dariyar datake tayi hankali kwance cikin farin ciki kamar ta dauwama cikin farin ciki haka harwarshen rayuwarta. Qamshinsa yashiga hancinta ta juyo ahankali takalli qofar suka hada ido murmushin dake fuskarta bai daukeba taci gaba da kallonsa soyayyarsa mai qarfi nasake shigarta musamman irin kallon dataga yana jefota dashi, Ahankali yaqaraso cikin babban palon yazo gabanta ya zauna kusada ita yana sake kallon Murmushi da farin cikin dake kwance fuskarta. Cikin tsananin farin ciki s salma ke kallonsu tace, Allah yadauwamarda farin ciki mai darewa a rayuwarku da abinda zaku haifa. Kallonta sukayi atare suna amsawa da amin acikin xuciyarsu. Sake kallonta yayi sosai zuciyarsa ke tsumayin son sake ganin dariyarta data dauki hankalinsa fiyeda komai. Ganin irin kallon da yake mata ta fara qoqarin miqewa ya riqe hannunta ta zame ta miqe ta nufi dakin s salma tashigewarta tana Murmushi. Da kallo yabita itakuma s salma nabinsa da kallo tana tausaya masa da irin soyayyar data hango yana yiwa rumanah sbd tasan atarihin mineelik soyayya itace mugun makamin dazai kashe mai ita ko tabarbare rayuwarsa sbd tana cikin asalin asalin masifar datake bibiyar masarautar musamman data hada da haqqin mutenan 6oye dabasa yafiya musamman ita rumanah dasukewa gujewar haihuwar namiji sbd nesantata da kujerar mulkin mineelik. Wani 6oyayyan murmushi yasaki Wanda zaiyi wuya ga gani ya miqe bayan sun 'dan taba magana da s salma Wanda gabaki dayan Rabin hankalinsa na cikin dakin s salma Wanda duk tana lure saikuma taji jikinta yayi sanyi sbd tausayinsa. Dakinsa yaje yayi wanka yayi sallah ya nufi gurin sultan jalaluddeen. Suhailat agurin ammy tayi zamanta tayi wanka itada yara da Carolina sukaci abinci tana gama sallolinta baccin gajiya yayi gaba da ita. Ammy Palon s salma ta nufa sbd ganin rumanah ta qaurace masu takoma can wanda tasan qila sbd suhailat su samu sakewa tabar nan din. Acan abinci sosai s salma tasa taci sbd maheer daya bar mata saqon ta tabbarda rumanah din taci abinci. Ammy data shigo kuyanga daya a bayanta daukeda qaton tray cikeda abinci masu qara lafiya kala kala tace a ajiye gaban rumanah dake zaune tana cin boiled vegetables. Cikin kulawa ammy tace, Rumanah saurake suhailat taci abinci hanacan tana hutawa. Kallon ammy tayi kamar zatayi kuka tace, Ammy gashi naci abinci naqoshi amma anjima zanci insha Allah. Sam ammy bazataso takurataba tace to ki tabbatarda anjima kinci. To ammy insha Allah. Har dare tana gurin s salma bata komaba ammy so biyu tana dawowa kawo mata abinci da samuwar dafaffiyar madara mai zafi Wanda suke famar dirka mata da wasu maganin haihuwa lokacinda ammy tagama bata saida hawaye suka gangaro mata ta riqe hannun ammyn cikin wani irin yanayi na tsananin qaunar ammyn tace, Nagode ammy sbd kinzamo uwar data kasa bawa maraicinah damar juya rayuwata, Kin maye duk wani gurbi da uwa take dashi arayuwata sbd kin qaunaceni tun ina a tsumman 'yar baiwa harna girma amatsayin baiwa nazamo mutum mai 'yanci ayanxu, Bazan taba sakamiki da soyayyar dakikeminba amma nayi miki alqawari bazan ta6a zama butulu mai manta akhairinki agareniba zan cigaba da zama tamkar baiwa agareki har qarshen rayuwata sbd kece kikabani abu biyu danafi so arayuwata 'yanci da...... Kasa fada tayi sbd nauyin ammyn saidai ko bata fadaba ammyn tasan maheer take nufi Tausayinta da sabuwar qaunarta tareda zancenta yasa jikin ammy mutuwa matuqa cikin sanyin murya tace, Rumanah ina qaunarki ne aranarda kika fado duniya tamkar 'yar dana Haifa nakejinki shiyasa nakeso kiyimin alqawarin komai zai faru har abada bazaki daina kallona kina tuno matsayina na uwa agarekiba wadda bazata taba yin wani abu dan cutatarwa agarekiba. Da hawaye a idanuwanta tace, Ammy nayi miki alqawarin har abada zan kare martabarki ta uwa dakike da ita agareni. Rungumeta ammy tayi tashin hankalinta da fargabarta tareda tausayin rumanah nasake ninkar mata. Har dakin dake palon s salma ammy taraka rumanah ta kwanta sukai saida safe ta fito ko tsayawa gurin s salma data shiru cikin jimamin zancensu ta fice. A palon ammy yaci abincin dare yana gamawa ya wuce dakinsa ya kwanta duk da zuciyarsa na kwadayin ganin 'daya daga cikin matansa. Washe gari qarfe goma na safe masarautar tacika da baqin mineelik Ethiopia sbd daukar matan yarima maheer uwayen magajin mineelik tareda sultana zaarah da aka mayar mata da matsayinta lokacinda labarin cikin rumanah ya isa ga sultan. Harda jakadiya da itace zata karbi ragamar kulada cikin rumanah tun daganan Libya harzuwa haihuwarta. Lokacinda aka fito da rumanah cikin wani irin shiri na adon doguwar royal gown cikinta yafito sosai tana tafe kusan bayi da guards goma zuwa sama Suna bayanta. Kallonta ammy tayi jikinta na sanyi Jakadiya ma cikin ta qarawa ido numfashinta na fita da sauri tasaki ajiyar zuciya. Gogan kuwa tunda yaga abubuwa sunfara canxa masa daga yanxu ya rintse ido tareda budesu yayiwa Jakadiya kallo 'daya tagano manufarsa ta qarasa ta tarbi rumanah din ta suka nufi motar da zaishiga aka bude mata tashige nan kowa yashiga motocin suka nufi airport. Tunda suka shigo motar hannunsu suke sarqe dana juna saidai babu mai iya magana acikinsu dan kowanne da halinda zuciyarsa take ciki. Ko acikin jirgi tafiyar babu Wanda yake iya magana acikinsu sbd kowa da abinda yake kai kawo acikin zuciyarsa. Suhailat dama tuntuni tasan ita farin ciki yaqare arayuwarta daga ranar da mijinta yafara son rumanah musamman yanxu datakejin duniyar dakomai ya fice mata arai gashi ciwon dakecinta yafara fin qarfinta musamman yanxu datake yawan ciwon mara mai tsanani. Qarfe hudun asuba jirginsu ya sauka a Ethiopia. Matse hannunta dake cikin nasa yayi ta juyo takallesa da idonta dasukai ja sbd tsananin damuwar dake ziciyarta. Ahankali ta zare hannunta ta miqe ta wuce gaba su Jakadiya da sauran suka mara mata baya tana qoqarin maida hawayen dake qoqarin zubo mata. Bayanta yabi da kallo idanuwansa na canxawa Hannunsa suhailat ta riqo idanuwanta cikeda hawaye cikin rawar murya da kulawa tace, Zan zamo bangon jinginarka aduk lokacinda kake buqatar hakan. Rintse ido yayi idanuwansa naqara canxawa suka fito jirgin. Motar rumanah daban ita kadai da masu tsaronta kuma itace agaba sai sauran nasu lokacin gari baigama haskeba. Ruwa yaji ankelaya masa yayi saurin bude ido yatashi a matuqar zafafe saiyaga jini kaca kaca a jikinsa da sauri yatashi tsaye aka mayar dashi zaune da qarfi tareda dora masa wata doguwar takobi mai tsananin kyallin sbd kaifinta tsoro bai kamasa sbd dama yasan hakan zata iya faruwa ko yau ko gobe.... Cikin wata irin murya data amsa amo har cikin qwaqwalwarsa yaji ance"""asauke kansa Daga gangar jikinsa a qawata qofar shigowa masarautata dashi kowa ya 'dan'dana kalar mulkin assultana the redblood Queen. Daga takobin akayi da qarfi za'a sare kansa yayi wani irin yunquri yana hada mugun zufan daya jiqa dukkanin jikinsa yakalli adama dake gefensa itama ta farko tana hada nata zufan da alama itama wani mugun mafarki tayi kamar shi sbd harma tafisa rudewa sbd rawar da jikinta keyi. Saukowa yayi kan lafiyayyan qaton gadonsa yanajin wani irin tashin hankali na shigarsa busar data cika masarautar tashigo kunnensa kenan su maheer sun iso. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: _*TARAYYA*_ _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *29* Not edited Daqyar tasamu tayi bacci sbd ciwon kai koda gari ya waye bata fitoba saida dukkaninsu suka fice aiki tafito daqyar tasha tea takoma daki tayi zamanta ko kallonma a dakinta tayisa duk da rabin hankalinta baya ga kallon. Daga office ma yau tare suka dawo da wuri sbd driver yaje yadauko suhailat suka biyo suka daukesa suka dawo gida tana kicin ta hango shigowarsu palo ta lafe taqi fitowa Suhailat na maqale da hannunsa suka wuce sama tana fada masa wani zance sai murmushi yakeyi harda shafo fuskarta. Harsuka shige bata daina kallonsu ba ta aje freshmilk dinda tazo sha takoma daki a sanyaye. Qarfe takwas da minti ashirin suke dinner Carolina tazo kiranta inji suhailat tazo suci abinci. Batai musuba ta miqe ta nufi qofa tafito. Tundaga nesa take hango wani irin kallo dayakewa suhailat dataci wani irin ado cikin wata doguwar riga mara hannu black sai qyalli takeyi tana masa magana tana dariya shikuma saidai ido. Riqo hannun suhailat yayi cikin miskilanci yace, Hmm my wife is this Talkactive and I don't know wow.. Murmushi tayi tareda yiwa hannunsa dake riqe da nata kiss tace, I love you maheer. Shafa fuskarta yayi yace, Ok time to eat. Juyawa rumanah tayi jiki sanyaye sbd zuwanta gurin zai rage musu jin dadine kawai musamman suhailat dataga tana cikin farin ciki sosai. Bayanta yabi da kallo a sace harta shige dakinta sbd tun fitowarta yaganta sbd dama hankalinsa na nutsuwarsa nakan qofar. Abinci Carolina tazo ta dibarwa rumanah babu Wanda yace tasake kiranta sukaci abincinsu suka yakoma sama suhailat taje ta taya Carolina shirin baccinsu amah. Yana kwance idanuwansa a rufe suhailat tashigo ganin kamar yayi bacci yasata komawa dakinta tayi kwanciyarta. Tundaga ranar rumanah taqara nesanta kanta dasu sbd ganin sunfara mantawa da wanzuwarta a gidan Dama aikinta yaqare tunda tasamu cikin da akeso. Sati 'daya kenan basu saka juna a ido ba sbd qauracewa musu datayi har gwara suhailat tana zuwa dubata duk tadawo aiki sbd sanin lafiyarta musamman yanxu da Cikin yaqara fitowa. Yau da wani irin ciwon kai da zazzabi ta wuni ko ruwa daqyar take iya sha sbd komai taci sai amai. Qarfe tara suhailat tashigo dakinta dubata taganta kwance lamo tayi shiru jikinta yayi matuqar zafi. Cikin kulawa da tausayawa tace, Subhanallah bakida lafiya haka shine baki fadaba. Cikin dasashiyar murya tace, Kaina ne yake ciwo sosai. Fita dakin suhailat tayi da sauri ta nufi dakinsa Koda tashiga yafito wanka yana zaune sanyeda wandon bacci mai tsantsi black bai sanya rigarba yacika dakin da qamshinsa da sanyin AC yaqarawa da'di yana zaune kan kujera ya dora qafafunsa kan table yana waya da ammy. Cikin 'yar damuwa tace, Baby rumanah batajin dadi sosaifa tace kantane yake ciwo sosai and the condition she's in kasan ba'ason tana fama da damuwar ciwo ko yayane. Aje wayar yayi batareda yakalletaba a miskilance yace, Mezan mata? Zaunawa tayi kusa dashi tareda dafasa tace, Baby pls kadubata kasan maganin dazaka bata baza'a barta cikin halinda take cikiba wlh daga gani kuka ta yini tanayi.... Wani kallo yayi mata jin abinda tace kafin ya dauke kai yace, Idan tabaki tausayi har haka ki kawota naga abinda zan iya yi. Miqewa tayi tafice cikin jin dadi. Daqyar rumanah ta tashi tabiyota tana tafiya ahankali sbd Sam har cikinta jitake yayi mata kamar ya kumbura ya danne saman cikinta. Koda suka isa dakin rumanah sauke kanta tayi har kusa dashi suhailat takaita ta zauna Shi ko kallon inda suke baiyiba yana duba Abu cikin laptop din dake gabansa. Cikin kulawa suhailat tace, Bari naje nasa carolina ta hado miki abinda zakici kafin kisha magani,ta fice. Shiru tayi numfashinta na fita da sauri jinta kusadashi sosai Shikuwa aikin gabansa yakeyi sai dai ganin yana neman fara shirme yasashi rufe laptop din yajuyo ya qura mata idanuwansa. Jin kallonsa na yawo ajikinta yasata 'dagowa ahankali takallesa nan take idanuwanta suka ciko da hawayen masifaffiyar kewarsa dake cinta. Yana kallo hawaye suka gangaro daga Cikin idanuwanta ya lumshe ido yasake budesu akanta Hannu ya miqa mata babu musu takama tareda fadawa jikinsa tana sakin kukan datake riqewa duk kwanakin. Rungumeta yayi tareda rufe ido yana jin nutsuwarda yarasa duk kwanakin tana dawo masa. Qanqamesa tayi tana sake shigewa jikinsa sbd sabuwar kewarsa dake shigarta dukda tana jikinsa din. Sun jima ahaka kafin ta dago fuska ta kallesa shima ita yake kallo tasaki murmushin cikar buri Ya shafo fuskarta zuwa lips dinta yace, Kukan da aka yini tanayi na ciwon gske ne kona kewar ammy ne? Soke kanta tayi sbd sarai tagano 'dan ammy yake nufi ba ammy ba. Murmushi yasaki sbd qin dago kanta datayi sbd kunyar zancen sbd ta tabbarda yariga yagane shine kukanta shine murmushinta. Dago fuskarta yayi tayi saurin rufe idonta ya zura hannu cikin rigarta ahankali yashafo cikinta Ta bude ido tana kallon fuskarsa. Da ido yanuna mata cikin yayi kicking tanajin motsin itama musamman yanzu da hannunsa ke kan cikin saitaji qaunar cikin da maishi sun sake shigarta ta dora hannunta kan nasa dake kan cikin suka kalli juna sbd sake motsi da Cikin yayi. Suhailat data shigo basusan tashigonba ta tsaya cak tareda kallonsu jikinta na 'dan rawa tayi saurin aje tray din tsakiyar dakin ta fice ko dakinta bata komaba dakinsu amah taje takwanta kusada fammah tareda Rungumeta ajikinta tana kiran sunayen Allah. Basuyi tunanin suhailat zata dawoba hakama basu lurada abincinda takawoba yabata fruits din dake gabansa wainada suhailat takawo masa tuni tasha kadan yabata magani tasha tana kwance jikinsa daganan ko mintuna nawa batayiba bacci ya dauketa dama akwai na bacci sosai aciki sbd yanayinta daya nuna bata samun isashen bacci. A jikinsa tayi bacci yazare mata doguwar rigar jikinta yazare mata bra yabarta da pant yasaka mata rigarsa ta bacci duk da ta mata mugun yawa ya kwantarda ita kan gado tareda rufeta bayan yayi kissing idanuwanta dake rufe. Kan kujera yakoma yabude laptop dinsa yanason cigaba da aiki amma yakasa yayi crossing legs yadauki fruits 'din data rage yana sha idanuwansa nakanta ya zuba mata yana kallonta nutsuwa nasake shigarsa. Washe gari kusan tare suka tashi hannunsa cikin nata suka shiga toilet sukayo alwala sukazo sukai sallah daganan bacci suka koma Wanda ita rabon datai irinsa ta manta shikuwa banda kallon fuskarta da cikinta babu abinda yakeyi daga baya yasake shigar da ita jikinsa ya lumshe ido bacci yadaukesa. Qarfe bakwai suhailat tayi shirin zuwa aikinta ta fice ko breakfst bata tsayaba apple kawai taci bayansu amah sun wuce school. Sai qarfe goma suka sauko tana gefensa sanyeda jallabiyarsa datai mata mugun yawa ta nufi dakinta da sauri sbd batason haduwa da suhailat da rigarsa ajikinta. Shikuwa black Gucci trouser ne ajikinsa da black shirt fuskarsa sosai take bayyanarda annashuwar da zuciyarsa ya nufi dining yana waya da sultan dake sanardashi abinda ya 'daga hankalinsa na cewar sufara shiri kowane lokaci zasu iya dawowa gida sbd rumanah a mineelik zata haihu. To kawai yace sbd kai karshen zancen dan zai iya samun matsala da sultan din idan yace aa. Wata doguwar Turkish gown tasaka Maroon wadda tayi mata kyau matuqa musamman da cikinta yafito tayi rolling kanta ta sanyo loafers black tafito tana fidda siririn qamshin daya zama tamkar na jikinta. Kai tsaye dining ta nufa itama tunkan taqaraso ya zuba mata ido yana kallonta musamman murmushin dake fita fuskarta dayafi 'daga masa zuciya. Tana zuwa kusada shi ta zauna tareda duba abincin ta zuba masa Wanda tasan yanaci ta dibi chips kadan taci da mango mango juice mara sanyi ko kadan sbd tuni yasawa Carolina dokar karta kuskura kaiwa rumanah Abu mai sanyi. Suna gamawa ta sanarda Carolina zata fita ta fice Kodataje yana cikin Mercedes-maybach exelero 'dinsa da alama shine zaiyi driving din Taqaraso tashiga sukabar gidan. Asibiti suka nufa,suna isa kai tsaye office dinsa suka nufa Suna shiga ya nuna mata quryar resting room din dake cikin office din yace tashiga yana zuwa. Shiga tayi taga harda 'dan madaidaicin gadon hutawa mai kyau a dakin sai couches da table harda TV da fridge ga split ac dake aiki Ta zauna kan couch tareda lumshe ido tana kallon hotonsa dake cikin qaramin frame kan table. Murmushi tasaki tareda 'daukar frame din qasan maqoshinta ta furta, Iwe dihalhu. Cikin kunnenta taji ance, I heard that. Saurin juyowa tayi tana ganinsa ta rufe idanuwanta cikeda jin kunyar kanta. Ya riqo hannunta yana murmushi ya nufi gadon dakin da ita yana cewa, Karki damu suhailat is kind hearted bazata hanaki mijintaba. Murmushi tayi tana zaunawa bakin gadon sbd har lokacin bata daina jin kunyar zancentaba. Janye rigarta yayi yafara scanning din cikinta cikin qwarewa harya gama yayi rubutun dazaiyi fuskarsa batadaina bayyanarda annurin da zuciyarsa take cikiba. Tayarda ita zaune yayi suna fuskantar juna ahankali yace, Babynki saura wata hudu yazo duniya yaga stubborn mom 'dinsa mai kishi da antyntah dabatasan tafita son mijintaba ba. Kallonsa tayi da sauri jin abinda yace bayan baisan meye sirrin tata zuciyarba saidai baisan tayi masa kyakkyawan saniba dahar tagano maganarsa is like yana challenging dinta akan sonda take masa. Murmushi tasakar masa tareda kai bakinta daidai kunnensa cikin wani irin salo ahankali ta furta, Kanason tabbatarwane? Wani irin murmushin jin dadin daya ratsa zuciyarsa yace, Tabbatarwar nake buqata. Murmushi tasaki mai qaramin sauti tareda qara 'dora bakinda kunnensa saidataja wani irin numfashin datasan zai 'daga masa hankali kafin cikin ra'da tace, Umarni ne ko buqata? Kasa haquri yayi saidaya ha'data da jikinsa ya shafi wuyanta yana sake sakin wani sabon qayataccen murmushin Shima qasa qasa yace, Duka. Tashi tayi tana 'yar qaramar dariyar data sake burgesa yariqota tadawo jikinsa cikin wani irin salo tana fadowa ta dora bakinta anasa bayan tayi qoqarin yakice kunyarta da qarfi. Cikeda mamaki da farin ciki mai tsanani yake kallon idonta tayi saurin rufe masa ido da hannunta 'daya Nan suka samu damar kissing juna cikeda kewar juna. Sai rana tsaka suka koma gida har lokacin suhailat bata dawoba babu kowa sai Carolina shiyasake basu damar sakewa a dakinsa sukayi abinda sukaga dama sukayo sabon wanka suka sauko cin abinci Ko a dining sosai yau Carolina take satar kallonsu tana mamakin irin abinda taga yana faruwa atsakaninsu. Koda suhailat tadawo suna sama batai shishigin zuwaba tayi wanka dakinta tashiryo cikin qananan kaya marasa nauyi bata fitoba sai lokacin dinner kuma suma lokacin suka sauko Rumanah na ganinta taji nauyinta sosai Shiyasa ko kallon inda yakeyi bata sakeyiba ta maida hankali gurin cin abincin ta hankali kwance. Suhailat ma bata nuna damuwar komaiba saima qoqarin ganin tasake data ringa mata. Suna gamawa suhailat ta matso kusa dashi ta ranqwafo tai kissing hannunsa tace, Gud night baby. Ta juya gurin rumanah dake qoqarin barin gurin tace, Gud night rumanah. Cikeda kunya tace, Allah yatashemu lafiya. Dakinta ta nufa tabarsu suna binta da kallon girmamawa. Da kansa yadauketa har zuwa dakinsa ya kwantar da ita ahankali kan gado batareda yace komaiba ya juya yashige toilet. Kwananta biyu agurinsa ranar na ukun tana sane da abinda suhailat ke nufi shiyasa tun wuri tayi kwanciyarta dan ko agurin dinner tariga kowa tashi tayi musu saida safe Shima yagane mai suke nufi shiyasa bai damuba ahaka suhailat tagama kwananta biyu saidai kuma kwanan biyu bata yisu cikin lafiya ba sbd wani irin zazzabi da ciwon kai datake fama dashi. Tashin farko dayayi mata test cikin wata uku ya bayyana ajikinta Wanda ya basa mamaki ta yanda bai taba luraba ita kuma dama tasan da abinta kawai taga tunda bana farko bane kuma akwai wadda tafita buqatar kulawa tunda ita natane na farko shiyasa kawai tabarwa kanta. Rungumeta yayi cikin nutsuwa yace, Thank you suhailat. Shafo fuskarsa tayi cikin qaunarsa tace, Why are you thanking me? Sbd you're always given me happiness. Murmushi tayi tareda taba hancinsa tace, Ka godewa Allah not me. Ina godewa Allah koyaushe daya bani best wife datake qaunata, Ina fatan komai na zama anan gaba zaki cigaba da sona bazaki barniba. Hakanan taji faduwar gaba tareda tausayin kansu tace, I promise to be with you and support you komai rintsi komai wuya koda akan abinda kakesone. Rungumeta yayi jikinsa da zuciyarsa na shiga wasi wasin komai zaizo gaban. Ranarda cikin rumanah yacika wata bakwai na suhailat yacika wata biyar mumman saqo ya iso daga mineelik na 'daukar rumanah da suhailat dan zuwa haihuwa. Lokacinda yakira ammy yasanarda ita atake tafara shirin komawa mineelik 'din tsoro da fargabar data danne na dawo mata sabo. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: _*TARAYYA*_ _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *31* Not edited. Kallon adama dake qoqarin saukowa gado yayi yaga yanda jikinta ke rawa saidai Sam bata tata yakeyiba mafarkinsa ya girgiza tunaninsa da zuciyarsa matuqa sbd su mutane ne dasuka yarda da mafarki, Basason 'yaya mata sbd muguwar aqidar dasuke ciki ta wani irin mulki da ake gudanarwa na tsantsar iko kowa yasan mulkin mace a mineelik masifa ce dabaza'aso maimaitawaba sbd jinin matansu bazai iya controlling na abinda yake tareda throne dinba kamar namiji shiyasa mulkinsu yake zama tamkar masifa ko annoba sbd mulkine na tsantsar zubarda jini Wanda babu yaro ba babba bare mata bare maza,ba tsoho ba tsohuwa. Alqawarine yadauka bazai taba bari mace ta mulki mineelik ba koda zai rasa ransane sbd yasan duk macen dazata hau zaiyi wuya basuyi ajalin junaba dayaga haka ya roqi Allah yayi gaggawar daukar ransa. Cikeda rudu adama takallesa tana goge fuskarta dahar lokacin take gumi tace, Sultan nayi mugun mafarkinda gwara nayi mutuwar qasqanci a hannun 6arayi dana fuskanci irin abinda Nagani a mafarkin. Bai kalletaba bare yatsaya sauraran abinda take fada sbd tunanin daya cika zuciyarsa akaro na farko arayuwarsa dayaji mulki yafara fita ransa sbd duba da irin mutuwar da sarakunan mineelik keyi yayi tunanin zai iya tsallakewa ya sauka mulkin salin alin batareda fuskantar irin qarshen sauran sarakunan ba shiyasa ya tattara duk dagewarsa akan ganin maheer ya karbi mulkin amma yaqi gashi matarsama ta haifi namiji arabasa da wannan masifar abu yaqi yiyuwa ta wani 6angare ga daular shiefffs na jiran rashin magajinsu su zamo bayi a qarqashinsu Wanda yafison ya sare kansa daga gangar jikinsa dayaga wannan baqar ranar yanzu kuma ga wata masifar nason 6ullowa sbd baisan me mafarkinsa na assultana yake nufi ba. Hannunsa ya daga ahankali ya shafo fuskarsa cikin mamaki saiyaga zufa ne ke tsatsafo masa, Rabon da yayi zufa a rayuwarsa harya manta. Irin tarbarda akayiwa isowarsu ta qara sanyaya jikin rumanah sbd tafara fargabar itama me zata Haifa sbd ganin irin dubban jama'ar dasuka dogara da abinda zata haifa. Lokacinda mamani tayi ido biyu da rumanah da cikin dake jikinta wani mugun jiri mai qarfi ya 'dibeta nuratu tayi saurin tareta tana kallon idanuwanta dake cikowa da qwallar baqin ciki tace, Mamani lafiya? Kasa riqe hawayenta tayi sbd baqin cikin daya rufe zuciyarta tace, Har abada bazanyi lafiyar zuciya ba sbd bulama da asma'u har bayan barinsu duniya basu bar kurwata ta zauna lafiya ba bayan duk balain dasuka sako rayuwata aciki dan haka wlh bazan zauna nashaqi numfashi mai dadiba sai ranar dana gama lalata dukkanin zuriar da suka bari aduniya.... Sakinta nuratu tayi cikeda mamaki da baqin cikin halin mahaifiyar tata muryarta na rawa tace, Mamani dazaki cire abinda yake ranki gameda rumanah dakin cire sbd zai kaikine matakin halaka sbd yanxu tariga ta taka wani matsayinda duk Wanda yayi mata wani ganganci zai iya rasa rayuwarsa sbd dukkanin burin daular nan da zagayenta akanta da cikinta yake dan haka ki nesanta kanki da ita sbd gujewa rasa rayuwarki..ke mahaifiyatace ina sonki fiyeda komai amma bazan iya kallo ki cuci rumanah ba dan haka karkiyi abinda zai barni da rashin zabi face na fadi gaskiyar dazaki rasa rayuwarki. Tana gama fadar haka tabar gurin cikeda damuwa Duk murnarta da farin cikin ganin rumanah din ya 6aci sbd mamani. Kukan 6aqin ciki mamani tasake tana tsinewa bulama da asma'u ta juya ta nufi gurin adama da sai alokacin zata fito tarbon. Kallo daya tayiwa cikin rumanah taji tari mai qarfi ya sarqeta kamar ranta zai fita take ta gigice da gudu akaje aka kawo mata ruwa ta karba tasha idanuwanta dasuka firfito sukai jajir sbd tari numfashinta na fita da sauri ta juya tabar gurin nanma idonta ya sauka kan na suhailat dake tsaye gefen Maheer ai take taji qaramar hauka na neman kama zuciyarta tana isa palonta na farko dukkanin bayi da kuyangin part din suka fice sbd gudun laifi lurada halinda take ciki. Mamani data sake biyota da ruwa ta miqa mata har lokacin itama jitake kamar ta cinnawa mineelik wuta kowa ya babbake ya mutu ko zataji abinda ya tsaya mata a maqoshi ya fada. Karbar ruwan tayi tasake sha tana cewa, Burina dana gina tun ina budurwa bazai taba rushewaba kan baiwa 'yar bayi, Babu Wanda bazan iya raba gangar jikinsa da kansaba kan burina sbd burina shine burin karagar mineelik.. Cikin tsananin damuwa da baqin cikin mamani daya kasa dannuwa aranta tace, Duk inda bulama da asma'u suka sauka saisun bar masifar data addabi kowa awajen Shiyasa bazan numfasaba saina tabbarda na tarwatsa rayuwar rumanah da abinda ke cikinta. Kallonta adama tayi da jajayen idanuwanta baqin cikinta na ninkuwa tace, Ko bulama ne aduniya bai isa ya shiga tsakanina da hawa throne din mineelik ba bare 'yarsa dan haka ni adama ayau ina sake daukarwa kaina alqawarin kawarda ko wanene ya shiga hanyata ta cimma burina Idan nace ko wanene ina nufin ko wanene ciki bancire kowaba. Cikin takaici mamani tace, Allah yasa gurin haihuwa ta mutu daga ita har abinda zata haifa kowama ya huta. Kobata mutu gurin haihuwa ba ta haifi namiji saiya mutu kozan rasa rayuwatane"""adama ta fada  tana miqewa tsaye. Tsayawa tayi tareda juyowa takalli mamani itama mamani ita takalla sai alokacin kowannensu yadawo nutsuwarsa jiki na rawa mamani ta zube tana sunkuyar dakai Adama fuskewa tayi sbd duk duniya daga ita sai bokanta ne suka San da sirrinta sai yanzu da 6acin rai yasata fadar abinda ke ranta saidai kuma ga alama tasamu wadda zata riqa amfani da ita Dan cimma burinta musamman da kusancinsu da rumanar zasuyi amfani tunda tana yiwa mamani kallon uwa. Wani irin babban sabon sashe da aka zubawa tsaro na musamman aka kaita Wanda yake gefen part din yarima maheer duk wani abin jin dadi da hutawa anxuba mata shi ga kuyangi na musamman da aka kawo mata. Bayan duk wata aladar tarbonsu anyi angama da daddare bayan tayi wanka ta saka kayan bacci ta kwanta bakin gado tareda lumshe idanuwanta ta bude ahankali tareda kiran sunansa cikin zuciyarta. Suhailat kuwa sbd yanayin jikinta da gajiya yasa tana kwantawa bacci ya dauketa cikin tsananin gajiya. Abincin da aka aikawa kowaccensu daga part din sultana zaarah babu wadda tasamu damar ci har gwara suhailat tasha madara mai zafi sbd sanyi datakeji kamar zai kamata. Rumanah kuwa kwance take tayi lamo cikin zurfi a tunani da tsananin son ganinsa sbd har lokacin takasa daina tuno yanayin dasuka rabu 'dazun hakan na raunana zuciyarta da kuzarinta ahaka bacci yadan 'dauketa tanayi tana farkowa hardai akai asuba tayi sallah takoma ta kwanta nanne tasamu baccin yadauketa sosai. Qarfe goma ta fito palonta anan ta tararda dining shaqe da kalolin abinci ta kalli qofa kamar tana jiran isowar wani hardai tagaji ta nufi dining tana fidda wani irin qamshi mai dadi. Fara cin abincinta kenan taji muryar data sakata dakatawa ta juyo da sauri suka hada ido da nuratu dake cikin tsananin farin cikin ganin rumanah din. Miqewa rumanah tayi zata nufeta Jakadiya data kawo mata nuratu din tayi gyaran murya dole ta tsaya tana kallon nuratu cikeda farin ciki Nuratu 'dince taqaraso gaban rumanah tana kallon cikinta tana sake bayyanarda farin cikinta zata zube qasa rumanah ta riqota tareda Rungumeta duk da tsinin cikinta baibari sun rungume juna sosaiba. Cikin tsananin murna rumanah tace, Tun jiya yakamata ace ke nafara gani da mamani amma shine kikaqi zuwa sai yanzu danace anemoki ina mamani? Baki washe tace, Mamani qila wani aiki ya hanata zuwa nima sbd tun jiyan nake yawo a hanyar sashen nan sbd kawai naganki amma bansamu damaba yanxu ana cewa kekenemanmu na aje aikina nazo bakisan yanda na matsu nagankiba rumanah nayi kewarki sosai kinbarni cikin kadaicinki... Hawaye suka sakata kasa cigaba da maganarta Rumanah ma hawayen ne suka ciko mata idanuwa ta riqe hannunta tace, Nayi kewarki nima nuratu saidai bayanda zanyine sbd kinsan da zabi ake bawa mutum nafison zama taredaku duk da ayanxu komai ya canxa arayuwata saidai matsayinku nanan keda mamani bazan ta6a canzakuba arayuwata. Murmushin qarfin hali nuratu tayi tace, Mamani bazata taba daukarki ayanda kika dauketaba. Ni zan cigaba da daukarta matsayin yayar mahaifiyata har qarshen rayuwata bazan taba duba abinda takeminba tunda na saba. Karkice haka rumanah sbd yanxu akwai banbanci bazanzo na rasataba sbd yi miki wani abu yanxu daidai yakeda rasa rayuwarta. Karki damu da wannan yanxu zo muci abinci tare nayi kewar hakan sbd bansaniba kozan sake samun irin wannan damar tacin abinci tare dake. Zama sukayi a babban dining din mai kujeru goma sha biyu nuratu na 'dar 'dar rumanah najanta da magana sbd tasaki jikinta ahaka sukaci abinci nuratu taci abinda takeso ta qoshi suka nufi palonta na qurya nan suka fara fira Nuratu takalli cikin rumanah dayayi mata kyau matuqa musamman sbd bai sakata qiba ba tsawo yayi sosai. Murmushi tayi cikin kulawa tace, Nayi farin cikin ganin rayuwarki ta canxa rumanah gashi zaki haifar mana 'yaya jinin sarauta. Kallonta rumanah tayi tasaki murmushi kawai sbd tunaninta ba akan firar tasu yakeba. Agurinta nuratu ta wuni sai tsakar dare ta tafi koshi da sharadin gobe Jakadiya zata saka acanza mata aiki adawo da ita gurinta. Mamani kuwa sunyi jiran zuwanta harsun gaji bata zoba gashi dokace akan rumanah bazata fita koinaba idanba da qwaqwaran daliliba harsaita haihu. Washe gari aka dawo da nuratu aiki gurinta duk yanda taso hanata aiki tabarwa sauran kuyangin qi tayi saidatayi. Kowace safiya da maraice sai Ammy ta Aiko mata da madara mai zafi itada suhailat harsukai kwana uku inda tun tana dannewa harsaida damuwarta ta daqushe kuzarinta matuqa dan ita kadai tasan halinda zuciyarta take ciki na rashin ganinsa gashi da alama bazata sake ganinsa ba saita haihu qila hakan ke sata kwantawa tayi kukanta sbd ji take nutsuwarta na neman gagararta abincima tun nuratu na iya yinta dan ganin taci har abin yafi qarfinta ta sanarda Jakadiya rashin cin isashen abincinda  rumanar keyi. Lokacinda Jakadiya taje ta sanarda ammy hakan yarima na tareda ita bai 'dagoba amma ammy kallo 'daya tayi masa tagano halinda yake ciki musamman dama tana lureda shikansa miskilanci da mulkine yahana agano halinda yake ciki na rashinta. Jakadiya tayiwa wani irin kallo nan take tagano me take nufi ta gyada kai ta wuce zuciyarta fal tsoro da mamakin irin sonda yarima kewa rumanah haka ta wuce taje kitchen ta bada umarnin ayi dukkanin girkinda akasan yarima maheer naso a shirya a palonsa na musamman zaici abincin daren tareda matansa. Da daddare koda Jakadiya tazo kiranta cin abinci cikin yanayi na  rashin walwala tace batajin dadin cikinta bazata iyacin abinciba yanzu sai zuwa anjima. Ba musu Jakadiya ta tafi Koda yafito cin abincin cikin wata irin shiga ta musamman ta kayan shan iska qamshinsa na fita ahankali. Suhailat dake zaune da cikinta ya kalla cikeda kewarta da tausayinta ya ware mata hannu ta taso ahankali tashige jikinsa ta rungumesa tareda sakin ajiyar zuciya. Cikin kulawa ya dagota tareda kallon fuskarta da cikinta ya shafi fuskarta ahankali yace, Hey hw are you? Murmushin mai ciwo tasaki na qarfin hali tace, Lafiya klau I missed you""ya fada tana zamewa daga jikinsa ta zauna kan dining sbd ita kadai tasan me ta hango a cikin idanuwansa. Zama yayi yana sake kallonta ganin jikinta yayi sanyi lokaci 'daya duk saiyaji lissafinsa na sake kwancewa abincin gabaki daya yafita ransa. Itama abincin fita ranta yayi saidai hakanan ta tsakuri kadan taci ta miqe tazo tayi kissing forehead dinsa tace, Gud night""ta fice tana mayarda hawayen idonta. Harta fice bai motsaba sbd damuwa da takaicin kansa dayaji akaro na farko. Saqone yazowa Jakadiya daga yarima maheer cikin gaggawa ta nufi sashen rumanah ta bada umarnin duk wata baiwa dake sashen rabarshi cikin mintuna biyu kacal. Babu 6ata lokaci dukkaninsu suka watse bayan koina yadauki sabon qamshi sai masu tsaron qofar shigowa ne kawai. Kwance take lamo bakin gado idanuwanta a rufe tayi nisa cikin tunani. Ahankali taji qamshinsa yana shiga hancinta ta bude ido tareda lumshewa zuciyarta na sake shiga damuwa sbd tasan har abada bazaizo sashentaba sbd atarihin sarautar mineelik ba'a taba yin sarki ko yariman dayaje 'dakin matarsaba saidai ita taje to mezaisa shi yazo gurinta. Shafo fuskarta yayi ahankali cikeda kulawa yana kallon kyakkyawar fuskarta tayi saurin bude idanuwanta dasuka ciko da hawayen ganinsa saita samu kanta da mayarda idanuwanta ta rufe. Rintse ido yayi cikeda mamakin kansa ya kamo hannunta ya riqe cikin nasa murya qasa qasa yace, Are you angry? Bude ido tayi takallesa sbd bata taba tunanin zai kulaba harya tambaya. Idonta dake kansa yakalla yana sake matse hannunta cikin nasa yace, Tashi zaune. Ba musu ta tashi zaune ya saki hannunta ya fito palo tabisa da kallo zuciyarta na qara mutuwa a sonsa, Jin soyayyarsa takeyi har cikin jini da ruwan jikinta kowane bugawar zuciyarta da sonsa take fita tana fata da roqon Allah yasa kar soyayyarsa tasakata kaucewa hanya takoina koda kuwa sonsa da kishinsa zasu kasheta. Jakadiya na ganin fitowarsa tayi saurin qarasowa tace, Allah yataimaki uban magajin mineelik akwai abinda ake buqatane? Hannayensa ya zuba cikin aljihun wandonsa cikin wani irin miskilanci yace, Ahado abincin cin mutum biyu. Cikin qanqanin lokaci ta dibi abincin cin mutum biyo ta jero a tray takawo masa ga mamakinta hannu yasa yakarba ya juya dakin yabarta da baki sake sbd tsananin mamaki. Duk yanda yaso tasakar masa fuska qi tayi yasamu ya lalla6ata taci abincin ganin shi baici ba yasata daukar abincin itama ta basa babu musu yaringa ci harsaidata kwatanci ya qoshi ta ajiye tana kallonsa da mamaki yadauki tray din yamiqawa Jakadiya dake palo ta fice da kayan. Brush yakaita har toilet tayo suka dawo ta zauna bakin gado ya zauna kusada ita tareda kallon fuskarta dahar lokacin take kadaran kadahan duk saiya rasa me ke masa dadi baimasan mezaice mataba sbd baisan menene yake faruwaba gabaki daya ta qarasa dame masa lissafi ya dafe goshinsa tareda rintse ido ya bude ya miqe zai tafi kawai yadawo yajawota jikinsa ya rungumeta batareda yace komaiba. Rungumesa itama tayi tareda barin hawayenta datake riqewa suka gangaro tana sake qanqamesa. Tun jekadiya na jiran fitowarsa harta gane ba fitowar zaiyiba tabar palon takoma palon farko ta dasa sabon jira. Tunda tabaro gurinsa mararta tafara ciwo ahankali tana shiga bedroom dinta takwanta tana qoqarin danne ciwon datake ji amma alamarin yafara qarfafa kafin tayi wani yunquri ciwon mara ya taso mata gaba 'daya gashi cikinta yanxune yashiga cikin wata na bakwai., Cikin qanqanin lokaci ta tabbarda naquda ce ta taso mata mai tsananin azaba sbd bata taba jin irin wannan ba a duk haihuwarta tun tana boyewa tuni yaci qarfinta koda Carolina taji kamar nishinta a dakin da sauri ta fita zuwa neman mutane duk da dare ya tsala sosai har anyi kiran farko. Asubar farin yabaro part din yakoma nasa ita kuwa zazzabi ne mai qarfi ya rufeta bayan wankan datayi da asubar amma bata nuna masaba saida ya fice takwanta tana rawar sanyi mararta na mata ciwo ahankali. Qarfe takwas na safe ta shirya daqyar tana daddaurewa sbd ta masa alqawarin zuwa gurin ammy yin breakfast su hadu acan. Nuratu na lureda kamar batajin dadi amma tayi shiru sbd ganin kamar batason yin ko magana suka fito suka nufi sashen sultana ana biyeda ita bayi kuwa sai zubewa sukeyi suna bata hanya cikin tsananin girmamawa. Jakadiya nacan tareda masu karbar haihuwa sashen suhailat hankulansu duk atashe sbd haihuwar  tazo mata da gardama matuqa Shikansa lokacinda labarin ya iso masa hankalinsa ya tashi dan haka ko gurin ammy bai nufaba ya kira doctors din dake karbar haihuwar kasancewar yasansu duka matane suke karbar haihuwa a masarautar in brief sukai masa bayanin haihuwa ce zatayi ta wata bakwai kuma tazo da gardama sosai. Kafin su isa sashen ammy ta lurada akwai abinda yake faruwa a masarautar sbd koina yayi tsit babu dogon motsi nuratu ce ta sanarda ita suhailat ce ke naquda. Faduwa gabanta yayi zuciyarta na cikeda mamaki da tausayin suhailar da ita kanta batace komaiba sai sanyi da jikinta yayi tana mata fatan haihuwa lafiya. Cikeda kaduwa da rashin sukuni ammy ta kalli Jakadiya tace, Ya Allah karabasu lafiya saidai ina cikin damuwa da fargabar yaya haihuwar rumanah zata zo itama Allah kadai yasan mezata haifa. Numfashi mai qarfi da sanyin jiki Jakadiya tasaki cikin rashin sanin abinyi itama tace, Mafita 'dayace itace idan har anason sirrin mutuwar iyayen rumanah yazamo sirri daga gareta muyi adduar kar asamu namiji daga gareta idanma ansamu namijin mutuwarsa itace mafita. Kallonta sultana tayi da sauri tana sake shiga rudu tace, Mutuwarsa na nufin qarasa bankado komai Wanda kinsan hukuncinda zamu fuskaanta agun sultan zaifi musan hanyarda zamubi musan wannan sirrin yacigaba da zama sirri kamar yanda sultan yafada tun farko... Saidai kuma zuciyata na quna da fargabar yanda zan fuskanci rumanah ranarda tasan mune sanadin mutwar iyayenta.... Da qarfi ruwan haihuwa suka 6alle mata lokaci 'daya sbd masifa da tashin hankalinda tashiga lokaci 'daya Cikin tashin hankali suka juyo cikeda mamaki da tashin hankalin abinda taji kafin suyo kanta ta durqushe agurin cikin tsananin azabar ciwon mara nan take naquda mai qarfi ta taso mata. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad @mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *32* Not edited _A gagguce_ Dafe cikinta tayi cikeda tsananin azaba da wani irin juyi da cikin keyi mata. Arikice Nuratu ta riqota tana kiran sunanta cikin tsoro da tashin hankali Su ammy atare sukayo kanta cikin sobon tashin hankali da fargaba Ammy ta riqota tana kiran sunanta cikin damuwa take kiran sunanta. A gaggauce suka kamata sukai sashenta da ita inda tun kafin su isa ta qarasa rikicewa sbd azabar naqudar. Cikin gaggawa Jakadiya ta isa gaban sultan dake zaune cikin royalhall suna jiran haihuwar suhailat ta zube qasa kanta qasa ta sanarda shi ummu-rumanah ta shiga naquda yanxunan. Da wani irin kallo ya dubeta zuciyarsa na shiga wani sabon farin cikin sbd yasan cikinsu biyun dole asamu namiji insha Allah. Wani murmushi yasaki na qasaita cikin nuna isa yace, Kije idan akasamu namiji a mineelik yau namiki na miki alqawarin dukiyarda bazaki iya qirgata da kankiba sai antayaki. Cikin fargaba tayi godia ta fice hankalinta tashe sbd daga ita har sultana a gigice suke basa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali sbd fargabar haihuwar rumanah dakuma babban sirrin dataji Wanda basusan ta yaya zasu fara fuskartartaba saidai abinda suka sani kome zatayi wannan sirrin bazai fadu garetaba babban tsoronsu da tashin hankalinsu kar Maheer yaji wannan alamari. Kai tsaye sashen yarima ta nufa lokacin yana zaune palonsa na farko zaune ya dora qafafunsa kan table din dake gabansa ya rufe idanuwansa kallo daya zaka masa kasan kadaici yake buqata baya buqatar hayaniya sbd yanayin naqudar suhailat dayake cinsa musamman yanda yasan ta wahala haihuwarta ta qarshe gashi yanxu har lokacin bata haihuba yana iya sensing azabar datake ciki. Gabansa Jakadiya ta tsaya tareda rusunawa cikin jimami tace, Allah yataimaki uban magajin mineelik uwardakina ummu-rumanah ta shiga naquda yanxunan.. Idanuwansa dake rufe ya bude ahankali ya zuba mata suna sake canxawa sbd dama tuni suka canxa sbd zaman jiran na kashesa., Miqewa tayi ta fice jikinta a sanyaye sbd gabaki daya ta rasa nutsuwarta jitake kamar zata zauce sbd fargabar tashin hankalinda zai biyo baya idan rumanah ta haihu ta tambayi abinda taji ayau din. Wayarsa daya kashe ya dauka ya kunna tareda kiran Dr ammenen muryarsa na bayyanarda tsananin damuwarsa da tashin hankalinsa yace mata tabar Dr noorah da nurse agurin suhailat taje gurin rumanah takuma babbatarda tana basa bayanin komai harta haihu idan kuma taga da damuwa takirasa kawai zaizo yakarbi haihuwar da kansa duk abinda zai faru yafaru. Aje wayar yayi zuciyarsa kamar zata buga, Yanxune yake sake takaicin haihuwarsu anan sbd acan shine zai karbi haihuwar kowaccensu da kansa musamman ita datake ta farkonta tana tsananin buqatarsa. Dafe goshinsa yayi ya miqe yayi ciki ganin kamar zai iya rasa hakurinsa yaje musamman dayaga anfara jan lokaci babu wadda ta haihu. Duk iya galabaituwa kowaccensu ta galabaitu sbd kowacce gadan gadan naqudar ta taso mata babu sauqi, Duk Wanda ke cikin mineelik hankalinta a tashe yake tsit koina ana jiran tsammani Sultan ma wannan karon saida hankalinsa yatashi shi fargabarsa kar doguwar naqudar tasa a rasa 'yayan dake cikin. Ammy duk inda nutsuwa da kwanciyar hankali suke basa tareda ita ko zama takasayi addua tajeyi tana qarawa musamman datake jiyo irin azabarda rumanar ke ciki sbd tana palo suna ciki tareda masu karbar haihuwar. Zufa mai zafi Jakadiya ta sharce lokacinda Dr ammenen takalli nurse tace, Get ready ga babyn nan fitowa yanzu Ku kawo komai kusa. Zufa Jakadiya ta gogewa rumanah data fice hayyacinta cikin tsananin tausayi da tashin hankali take mata sannu. Cikin wata irin rikitacciyar azaba tayi wani irin nishi mai qara Atake baby ya fado Dr ammenen ta qarasa jawosa tareda yanke uwa ta 'dagasa sama ya buga wani irin kukan jarirai babu qaqqautawa. Kadan yarage Jakadiya bata fadawa rumanah ba sbd rudewa da ganin abinda aka haifa. Miqa mata shi Dr tayi jikinta na matuqar tsuma ta karbesa aka nado cikin farin zanin auduga mai tsananin laushi ta qura masa ido tana jera ajiyar zuciya ba qaqqautawa. Wata sabuwar azaba ta tasowa rumanah cikin tashin hankali Dr takalli cikinta tana cewa nurse wani babyn na zuwa. Jiki na rawa Jakadiya ta fito ammy data jiyo kukan jariri ta matso bakin qofar jikinta na 'dan rawa zuciyarta kamar zata fado sbd bugawar datakeyi a qofar sukayi karo da jakadiya hannunta na rawa ta karbi jaririn tana qoqarin budewa taga menene cikin rawar murya Jakadiya tace, NAMIJI NE. Da sauri ammy ta dago ta kalleta tareda hadiye yawu ta qurawa yaron ido jajir dashi babu inda ya dauko rumanah Sak maheer ne saitaji bazata iya cutatar dashiba. Nurse ce tazo ta karbesa sbd aankeshi dazasuyi su kintsashi kafin dayan babyn yafado sbd naqudar takoma qasa tsananin wahala take sha ko ayanxun. Jiki na matuqar 6ari Jakadiya ta isa qofar sashen maheer tun a qofar ta zube tareda 'daga murya tace, Allah yataimaki uban magajin mineelik ummu-rumanah tasauka lafiya ansamu magajin mineelik da yardar Allah. Zabura yayi daga kishingiden dayake yana sakin ajiyar zuciya da qarfi yana rufe ido sbd zaman jiran dayake shine abu mafi azabtuwa a tsawon rayuwarsa ayau ya raina zamtaowarsa likita tunda bai taimaki matarsaba lokacinda takeda tsananin buqarsa. Fitowa yayi cikin wata irin qasaita hannuwansa zube a aljihunsa ya tsaya nesa da jakadiyar yana kallonta kamar tana daukeda abinda aka haifar yace, Kije ina miki albishir da zama jakadiyar magajin mineelik tareda kyautar werik'i(gold) Murna fal cikin ranta tace, Ameseginalehu(godiya) Miqewa tayi zata fita abakin qofa taci karo da 'yar saqo daga sashen suhailat ta durqusa qasa cikin girmamawa da rawar jiki tace, Gimbiyar yarima ta sauka ansamu NAMIJI saidai likita tace sanarda yarima bazata sake haihuwaba mmahaifarta tasamu matsala wannan itace haihuwarta ta qarshe. Zaro ido Jakadiya tayi cikeda tsananin mamaki da farin ciki tareda tausayin suhailat tajuya takoma gurin maheer tasanar dashi atake ya sake lafta mata wata kyautar zuciyarsa na harbawa da qarfi Ya zauna ahankali tareda lumshe ido yana yiwa Allah godia. Koda Jakadiya takoma sashen rumanah haihuwar tazo gadan gadan nan wani babyn ya fado Dr ta ciresa nanma sukaga namiji atake aka shiryasu jikin Jakadiya babu inda baya rawa ta zube gaban sultan kanta qasa cikin tsananin farin ciki tace, Allah yataimaki kakan magajin mineelik ummu-rumanah ta sauka lafiya ansamu 'yan biyu duka MAZA sai gimbiyar yarima itama ta samu 'da namiji Ina yiwa sultan farin cikin ganin wannan rana mai tarin cikar buri da biyan buqata, Ayau mineelik ta samu qaruwar 'yaya uku uku duka maza ina sake taya sultan murnar ganin wannan rana. Wani irin murmushi yake fitarwa mai bayyanarda farin cikin da zuciyarsa ke ciki bamai misaltuwa bane Dukkanin Wanda ke royalhall din farin cikine mai tsanani a fuskarsa nan take aka buga bell din mineelik aka sanarda haihuwar magajin mineelik atake labarin farin cikin ya bazu koina Ethiopia ta dauka kowa farin ciki yake da wannan burin na qasar daya cika. Dayake ba qaramar wuya dukkaninsu suka sha ba ana kimtsasu sai bacci banda rumanah data rufe idone kawai zuciyarta cikeda tashin hankali da fargaba tareda baqin cikin abinda kunnuwanta sukaji mata ammy na fada da bakinta. Hawayen idonta suka gangaro batareda tadamu da gogesuba ta bude idanuwanta dasukai ja hawayen nacigaba da 6alle mata., Idan kunnuwanta sun jimata daidai ammynta ke fadar sune suka kashe mata iyaye kenan ba mutuwar Allah sukayiba qarfi da yaji aka rabasu da rayuwarsa,aka rabasu da 'yarsu,Ashe shiyasa aka 'yantasu??? Girgiza kanta tayi hawayenta na tsananta tace, Ammy bazatayi hakaba nice banji daidaiba,ammy bazata iya kashe kowaba bare iyayena. Sakin siririn kuka tayi tareda kifa kanta a pillow. Suhailat kuwa bacci tayi sosai sbd ta galabaita fiyeda yanda ta tsammata saidai tana haihuwar taji batajin komai. Lokacinda aka kaiwa maheer yaran duka yana tareda khaleefa daya iso ranar khaleefa ne yakarbi sauran biyun maheer kuwa Wanda aka fara haihuwa ya karba akaro na farko dayaji jikinsa yayi sanyi sbd soyayyar yaron dayaji shima yau yahaifi magajin kansa bama na mineelik kawaiba. Qura masa idanuwansa yayi ganin yaron shine Zak sai lips din mahaifiyarsa daya dauko ya sa hannu ahankali ya shafo lips din tareda sakin wani irin murmushi qasa qasa yayiwa yaron addua kafin ya furta, ABEEL HASSAN. Kallonsa khaleefa yayi cikeda farin ciki ya maimaita sunan yana jinjina kai kafi ya karbesa ya miqa masa babyn suhailat da ba'ason motsasa sosai. Qura masa ido yayi cikeda tausayinsa da qaunarsa mai qarfi shima shiya dauko Zak saidai zamansa qarami sosai yasa yafisu haske. Addua yamasa sosai cikin rada rada ya furta, Jemaal. Koda ya karbi Hussain din abeel abrar bayan yamasa addua ya rada masa, ABEEL HUSSAIN Koda aka kaisu gurin sultan kowa saida yatabbatarda yau ranar daban take arayuwarsa ya 'dagasu daya bayan daya yayi musu addua kafin aka sanar dashi sunayen da yarima maheer ya rada musu sultan mai damuba sbd ayau angama masa komai arayuwa ya 'daga abeel cikin babbar murya yace asanarda kowa ga magajin mineelik ABEEL HASSAN. Atake akaje dakin tarihi aka saka sunansa da sunan mahaifiyarsa nan aka fara shagulgulan haihuwar. Har dare ammy bata samu ganin rumanah ba sbd tunda tayi wanka take rufe a dakinta tace bata buqatar kowa Hutu take buqata. Lokacinda aka kawo mata yaranta qura musu ido tayi hawaye na gangaro mata sbd idan bar aka iya raba iyayenta da ita za'a iya rabata da 'yayanta saidai batajin hakan zata iya yiwuwa koda zata rasa rantane. Rungumesu tayi tareda rufe ido qaunarsu data mahaifinsu na shigarta tako ina. Da daddare lafiyyan abinci kala kala aka aika gefen kowaccensu aka jera. Duk yanda Jakadiya da ammy sukaso ganinta qin bari tayi ta dasun shigo zata rufe ido tana bacci idan sun fita zata cigaba da kukanta. Kukane takeyi na rashin Sanin abinyi sbd ko ganin kowa batason yi. Lokacinda labarin haihuwar tasamu adama da 'yar dakinta mamani kadan yarage adama bata yanke jikiba mamani kuwa kasa daurewa tayi saidatayi kuka taji sauki sauqi cikin ranta. Koda aka kawo mata yaran saka musu albarka saidata kai zuciyarta qololuwa gurin bugawa kafin ta iya kallonsu idanuwanta na cikowa da hawayen baqin ciki tasaka musu albarkar dole. Suna fita ta miqe batareda takalli mamani dake matsar hawayeba cikin tsananin tashin hankali tace, Duk yanda za'ayi ayi yaran nan bazasukai ranar sunansuba batareda sunbar duniyaba kije yanxu ina buqatar kadaici gobe zan fada miki abinda zakiyi sbd inason alhakin mutuwarsu ya rataya akan kakarsu da jakadiya sbd inason qulla gaba mai tsanani tsakaninsu da yarima tareda matansa kuma inason sultan ne da kansa zai yankewa sultana hukuncin kisa ta yanda abin zai riqa bibiyarsa yana damunsa da haka zansamu sauqin aikina akansa. Acikin daren yakira suhailat yaji yajikinta tareda jemaal duk da khaleefa yadubasa sosai yafadi dokokin daza'abi kafin suna shi dole za'a koma Georgia dashi sbd yanayinsa acan za'a fara kula dashi. Duk yanda yaso ganinta yasan abune mai wuya saidai kuma bayajin zai iya bacci bai dubotaba bayan baqar wahalar dayasan tashiga yau gurin haihuwa saidai koda ya aika asanarda Jakadiya taje tayi ma sashen isonsa ta sanardashi har lokacin bata fitoba taji jiki sosai hutawa takeyi haka ya hakura saidai asubar fari ya isa dakinta lokacin tana zaune bakin gado tasaka yaran agaba hawaye nabin fuskarta. Qamshinsa yasata rintse idanuwanta hawayenta na sake gudu. Zama yayi kusada ita tareda riqo hannunta baice komaiba ya kwantarda kanta jikinsa sai kawai tasaki kukan datake ruqewa ahankali Cikeda mamaki da damuwa ya kalleta zaiyi magana ta zame daga jikinsa tana tsaida hawayenta cikin dasashiyar murya tace, Kaina na ciwo ina buqatar hutawa. Da mamaki yakalleta saidai baice komaiba ya miqe ya fice Ta saki sabon kuka cikin rashin Sanin abinyi. Duk inda hankalinsu ammy yake yatashi dashi kansa maheer din sbd kwana uku da haihuwar ko kadan rumanah takasa bari ko 'dayansu ya ganta duk wani tashin hankali suna ciki Ta hargitse tarasa abinyi gabaki daya ta birkice shikansa ta hanasa ganin kanta bare yasan meke faruwa babban tashin hankalin daya riskesu shine sanarwar da akayi za'a bawa uwar magajin mineelik kujerarta ta uwar sultan. Sam ammy ta rasa ina zata saka kanta shikansa baya cikin nutsuwa sbd bazai taba bari ta karbi sunan uwar sultan ba gashi dole zata karba itace zata bawa duk Wanda takeso riqon kwarya. Yau kwanansu biyar da haihuwar dukkanin yaran suna sashen ammy tun safe. Tunda sukazo abeel hassan ke kuka sosai anmayardashi gurin hamaifiyarsa saima qara birkicewa da yayi nan hankula suka tashi tuni sultan yasa atara duk masu magani da likitocin mineelik amma sai qara rikicewa yakeyi nan hankalin rumanah itama yayi masifar tashi ta rikice. Cikin tashin hankali suka dunguma zuwa royalhall inda ake duba yaron kowa hankalinsa atashe yake. Kallo daya yayiwa rumanah yaji lissafinsa yasake kwancewa kafin yayi wani yunquri sarkin gida yossouf Kaleb yashigo jikinsa na matuqar rawa ya zube gaban jakadiya yayi mata magana qasa qasa hankali tashe jikinsa na wani irin mazari. Zaro ido Jakadiya tayi cikin sabon tashin hankali jikinta yadauki muguwar rawa kowa hankalinsa nakanta anajiran jin saqon menene Ta zube gaban sultan tareda sauke kanta jikinta na tsananta rawa cikin muryar tashin hankali da tsananin fargabar rasa rayuwarta tace, Allah yataimaki sultan ina cikin baqin cikin sanardakai ankama baiwa mamani da dafin baqin maciji tabawa abeel Hussain da jemaal antabbatarda sun rasu saidai ankamata. Rumanah dake zaune ta miqe a firgice jikinta na rawa saidai ko daga qafa batayiba ta yanke jiki ta fadi agurin. Cikin tashin hankali yayi kanta kai tsaye yadauketa yabar palon su ammy na mara masa baya hankali tashe musamman sultana da a sashenta suke shaf tashin hankalin abeel hassan yasa suka mantasu acan. Sultan kuwa numfashi ya sauke cikin wani irin yanayi ya miqe tsaye idanuwansa na canzawa. Suhailat na zaune tana shan magani daqyar sbd ciwon ciki da jirin datake fama dashi tun safiyar yau din Jakadiya ta shigo mata. Murya na rawa tace, Ina neman afuwar saqon baqin cikin danazo dashi Allah yakarbi ran jemaal........ Bata qarasaba suhailat ta miqe tsaye atake jini ya 6alle mata ta yanke jiki ta fadi. #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *33* _A gaggauce_ Cikin tsananin tashin hankali Jakadiya tasa akayiwa Dr ammenen kiran gaggawa koda ta iso itama hankalinta tashe yake da jin abinda yafaru atake suka fara qoqarin tsayar da jinin daqyar yarage zubowar sosai saidai bata farkaba sbd allurar dasukai mata sbd jininta yayi matuqar hawa mai muni idan ta farka awannan halin zata iya samun paralyz. Sai bayan sunbaro gurinta aka sanarda maheer abinda yasameta lokacin yana qoqarin ganin rumanah ta farfado sbd duk iya abinda zaiyi ta farfado yayi bata farfadoba tashin hankalinda yake ciki yanxu yafi kowane tashin hankali na rayuwarsa, Rasuwar yaransa gakuma halinda rumanah take ciki yanxu kuma ana fada masa suhailat ma...dafe goshinsa yayi tareda fitarda numfashi mai qarfi da zafi idanuwansa na sake canzawa. Ammy sbd tashin hankalinda take ciki ko tsayuwa sosai bata iyayi tsaye take gaban gawarwakin yaran a palonta kallo daya tayi musu ta dauke kai hawaye na ciko idanuwanta sbd ganin yanda kalar jikinsu takoma mai duhu sbd dafin daya shiga jini da jijiyoyinsu sosai. Zaman dirshan Jakadiya tayi tareda dora hannu 'daya akai tana jinjina wannan baqar rana data zo musu koda suke tsananin buqatar haihuwar maza gashi ansamu mazan amma tun ranarda aka fara naqudarsu masifa tafara saukar musu saidai wannan masifar dasuke ciki yanxu mai hadari ce sbd koda misali sunanka yafito cikin wannan zancen mutuwace hukuncinka.. Jikinta na rawa ta miqe ta dauki gawar su biyun ta nufi fada qafafunta na wani irin rawa daqyar ta iya kai kanta gaban sultan ta zube tareda shimfidesu ahankali tana furta, Tuba nake da kawo mugun gani gaban sultan da muqarabansa. Kallo daya yayiwa likitan gargajiyansu ya taso yazo gaban yaran ya durqusa yadauki abeel Hussain yadubasa tareda zura hannu cikin bakinsa ya Ciro yakalla ya kalli sultan ahankali ya sunkuyar dakai ya girgiza kai alamar yariga ya rasu. 'Daukar jemaal yayi yaduba shima ya tabbar musu da yarasu. Atake sultan yakalli kaleeb cikin zallar 6acin rai da nuna ikonsa yace, Akai mai laifin kurkuku mafi tsanani ahadata maciji mafi hadari har zuwa gobe kafin tafadi Wanda yasata sbd bayin kantabe batada isar dazata iya yiwa ko bawan mineelik kallon banxa bare iya kashe jinin sultan. Cikin zaquwa kaleeb yace, Angama sultan...ya fice yana kwatanto irin azabar dazasu ganawa mamani. Cikin wani irin mummunan yanayi na firgici da tashin hankali ta farka tareda miqewa zaune jikinta na bata irin rawa tafara qoqarin tashi yayi saurin riqeta yana son kallon cikin idonta amma taqi tsayawa gabaki daya bata cikin hayyacinta fixgewa takeyi da qarfi yasake riqeta tareda girgizata da qarfi yakira sunanta. Tasaki wani irin kuka mai qarfi tareda fixgewa daga jikinsa ta zube qasa tafara kuka sosai tana qanqame jikinta sbd wani irin ciwo da ra'dadi mai zafi takeji cikin ranta kamar zuciyarta bazata iya daukaba. Sake riqota yayi ya rungume jikinsa da qarfi duk yanda taso qwacewa kasawa tayi tacigaba da fidda kuka mai radadi. Wani irin ciwo da baqin ciki  takeji na cin zuciyarta numfashinta har sarqewa yakeyi gurin kukan. Kasa magana yayi sbd radadin da zuciyarsa ke ciki na rashin 'ya'ya biyu lokaci 'daya dakuma ganinta cikin wannan halin. Ammy kallon Jakadiya tayi idanuwanta na qoqarin boye qwallarta tace, Ya akayi mamani tashigo nan harta bari aka kamata domin na tabbarda tana sane tabari aka kamata akwai abinda take nufi da hakan Wanda shine tashin hankalina., Meyasa bata kashesu a dakunan uwayensuba sai agurina? Innalillahi, allahumma ajirni fi musibati Wannan wace irin masifa ce mai wuyar cinyewa. Cikin sanyin jiki a raunane Jakadiya tace, Alqawarin Allah ne zai tabbata sbd sbd ayanxu alamu sun fara bayyanar mulkin mace a mineelik Wanda hakan na nufin ba'a zubarda jiniba yanxune za'a zubar dashi. Girgiza kai ammy tayi da sauri cikin tsananin fargaba da rudu tace, Rumanah bazata taba zama mai zubarda jinin bayin Allah ba, Nayi gudun haka kowa yakasa fahimtata, Na roqi Allah a zuci da fili akan kar rumanah ta haifi namiji idanma ansamesa yazo babu rai amma hakan bata faruba yanxu bansan ta ina kuma wannan masifar ta 6ullo ba. Duk yanda yaso ganin rumanah tadawo nutsuwarta abin ya gagara saima zuru datayi da ido kukan yadaina fita saidai hawaye kawai ko motsin kirki bata iyayi ta rakube gefe guda ta takure kanta. Lokacinda aka shigo aka sanarda ita zuwan ammy dubata bata motsaba saima rufe idanuwanta datayi hawayen ciki suka gangaro tunani abubuwa da dama na dawo mata, "" mafita 'dayace karta haifi namiji idanma ta haifesa mutuwarsa itace mafita"" "" yaya kike tunanin zan fuskanci rumanah ranarda ta San cewar mune sanadin mutuwar iyayenta"" Rintse idanuwanta tayi da qarfi nauyi da zafin zuciyarta na qaruwa saidai batason barin zancen yashigeta a irin yanayin datake ciki yanxu sbd tanason tayiwa ammy fahimta mai kyau bazataso abinda kunnuwanta sukaji mata ba yazama gaskia. Ammy kasa haquri tayi ta nufi dakin lokacin maheer yaje dubo suhailat. Har ammy taqaraso gabanta bata motsaba daga inda take takure idanuwanta jajir. Cikeda tsananin kunya da tausayinta murya na rawa tace, Rumanah har abada bazan iya cire qaunarki arainaba sbd qaunace Allah yasakamin cikin raina Wanda kisani har abada bazan iya yin abinda nasan zan cutatardake ina fatar zaki riqe hakan aranki...Allah yaji qan abeel Hussain. Juyawa tayi ta fice jikinta asanyaye sbd tana iya hasaso wasi wasi azuciyar rumanah. Tana fita rumanar sulale ta kwanta agurin tasaki sabon kuka tana dafe qirjinta dake mata zafi da wata irin tafasa. Cikin wata irin kaca mai tsananin nauyi da zafi aka na'do mamani da nauyin kacar yasata tafiya ahankali a duqe sbd ko qafarta daqyar take dagawa sbd nauyin kacar datake 'daureda ita. Aka bude wani tsohon kurkukun dayafi shekara goma ba'a shigesaba aja jefata ciki da qarfi kanta ya bugu da bango take goshinta ya fashe da jini ta fitarda numfashi daqyar sbd azaba gashi batada hannun shafawa taji sbd irin 'daurin da'akayi mata ko numfashi daqyar take fitarwa. Ta lumshe ido cikin azaba ta bude idon takalli qofar dishi dishi take gani sbd ba qaramar buguwa tayiba gashi anyi mata wani irin duka na rashin imani dan kariya biyu akayi mata a hannu 'daya. Wani irin kwando aka bude tareda jeho abinda ke ciki aka rufe qofa Wani irin baqin maciji tagani ya bude kansa yana fitarda huci. Mummunar faduwa gabanta yayi wasu irin hawayen azaba da tsoro tareda baqin ciki suka gangaro mata jikinta ko qarfin dazaiyi rawa bashidashi sbd ti6is akayi mata. Tana kallo macijin ya kwantarda kai yayi cikin wani qaton rami dake gurin Wanda shikansa ramin baza'a rasa wani macijin acikiba ko abinda yafisama. Maganarta da adama ta tuno tana fargabar kar komai yaqi tafiya yanda suka tsara. """ idan kikai nasarar basu wannan dafin suka sha zasu mutu atake kuma ki tabbatarda ankamaki duk wuya da azaba karki ce nice kice sultana ce Wanda kowa yasan hukuncinta na kisa ne kafin akasheta za'a bani matsayinta na sultana nikuma zanyi amfani da wannan matsayin na hana akasheki kuma daga lokacin namiki alqawarin matsayin Jakadiya kintashi daga baiwa har abada saidai kuma idan kika fadi sunana kisani babu 6ata lokaci dukkaninmu za'a kashemu amma idan kikace itace nizan kubutar dake kinga burinki na shekara da shekaru yacika ga 'yanci da dukiyar kanki dazaki tara"""" Numfashi tasaki a wahalce tana sake qarfafawa zuciyarta dan cika sauran aikin dan kuwa koda ta mutu tasan burinta akan zuriar bulama da asma'u yacika. Suhailat data farfado ahankali hawaye kebin fuskarta suna sauka kan qirjinta idanuwanta arufe sbd ko hannunta daqyar take iya motsasa. Qunci ne arayuwarta da zuciyarta, Rayuwarta ta lalace batada wani sauran farin ciki, Ta rasa mijinta badan ya rasuba, Ta rasa rayuwar aure mai farin ciki, Ta rasa lafiyarta, Ta rasa mahaifarta gurin haihuwa ga abinda ta haifa ta rasashi mai zaunawama ya rungumeta ya rarrasheta ta rasa Wace irin rayuwace mai tattareda garari take ciki? Wani irin kuka mai qaramin sauti tasaki zuciyarta na mata ciwo mai tsanani Kewar iyayenta da 'yayanta takeji sbd sune kadai sukasan zafinta da damuwarta. Qarasawa yayi bakin gadon tareda Rungumeta da sauri yana jin tausayinta fiyeda kansa sbd yasan tafi kowa cutatuwa sbd tafi rasawa tunda ba wata haihuwar zata sakeba. Akaro na farko arayuwarta taji batason kusancinsa agareta sbd nauyi hakan ke qarawa zuciyarta saidai ko motsi sosai bata iyayi bare ta zame jikinta hakan yasa wani sabon kukan qunci zuwar mata ahankali. Sosai ya lurada batai farin ciki ko jin sanyi da ganinsaba akaro na farko arayuwar aurensu daya hango wani yanayi daban akansa wanda ba sonsa bane atareda ita ya rufe ido cikin wata sabuwar damuwar yanajin tausayin kansama sbd wata jarabawace Allah yake jarabtarsa da ita akan rumanah wadda idan baiyi taka tsantsanba zai tashi da Rabin jiki ranar lahira saidai kuma baisan yaya zaiyiba sbd sonta yazama halitta ajininsa. Ahankali ya furta, Allah yaji qan jemaal. Sakinta yayi ya miqe tareda ficewa batareda ya qara kalma 'daya ba. A wannan daren mineelik ba kowa yasamu damar kwantawaba bare ya rintsa sbd dukkanin dole da masautar na cikin tasa kalar damuwar. Rumanah dai duk yanda akayi da ita taci abinci ko motsi taqiyi daga inda take idanuwanta sun bushe sunyi jajir ko gani sosai batayi sbd kumburin idanuwanta., Suhailat kuwa har lokacin bata iya kwakwaran motsi sai hawaye da ciwon qirji dayake cinta ita kanta anyi anyi taci abincin amma ko bude ido taqiyi sai hawaye take zubarwa. A rayuwarsa wannan ne karo na farko dayaji yayiwa sarauta da gidan sarauta wata irin muguwar tsana sbd yasan son mulkine yasa akai hakan, Ya tabbatarda kisace ta tabbata akan baiwar datayi da wainda suka sakata saidai bayajin zai tsaya ganin hakan gobe zaayi hidimar radin sunansu a goben zasubi jirgin dare su koma dan idan yananan zuciyarsa zata bugane da halinda matansa suke ciki musamman suhailat datake buqatar kulawa sosai. Ammy da jakadiya kusan a zaune suka kwana ko ruwan arziki babu Wanda ya iya sakawa maqoshinsa sbd tashin hankalin dazai iya faruwa gobe sbd duk Wanda sunansa yashiga koda misali ne cire kansa ya wajabta gashi a sashen ta abin yafaru shine babban tashin hankali da damuwar dasuke ciki musamman dasukasan wacece mamani. Ayau mineelik acike takeda duk wata masarautar dake zagaye da maqwaftaka da ita tareda wasu sarautun wasu qasashen da dama sbd gabatarda sunan magajinnta dakuma miqawa uwar magajin mineelik kambun saukewa da 'dora sabon sultan. Wannan matsayin daza'a bata ayau shine abu mafi ha'dari da tashin hankalinda yake ciki ayau Ammy duk yanda taso daurewa kasawa tayi saida hawayen baqin cikin datake ciki suka gangaro mata tun a daren jiya ta hana su ganta bare ta sanarda ita hadari da kuma illar abinda zata fada. Saidai alqawarine shi ya daukarwa kansa zai tabbarda ta miqa mulkin nan ga sultan ya dauketa sunkoma adaren yau din. Lokacinda aka hallara dan qaddamarwa saqo ya isowa sultan uwar magaji batada lafiya bazata iya fitowa. Kai tsaye aka fara qaddamar da komai aka radawa abeel Hassan sunansa tareda qaddamar da sunan ummu-rumanah acikin littafin tarihin mineelik amatsayin uwar magaji. Nan take masu rubuta tarihi aka bude paging fara rubuta nata. Daga ammy har yarima maheer babu Wanda ya halarci taron kuma sarai sultan yagano manufarsu tayin hakan zasu fuskanci hukuncinsa daga baya ayanxu baiwa mamani ce agabansa zai bata wata irin mutuwa mai firgitarwa itada wainda suka sakata ga 'yan baya. Koina yayi tsit jiran hukuncin sultan akeyi lokacinda mamani ta tabbatarda Jakadiya ce tasakata amatsayin itama sultana ce ta aikota. Tsita akayi  kowa wuta ta dauke masa musamman sultan da mamakin baiwa mamani yakamasa sbd yafi kowa sanin sultanarsa bazata aikata hakanba, Tabbas wannan baiwa mai taurin raice saidai ji da ganin hukuncin sultan kawai tajeyi batasan waye sultan ba. Kallo daya yayiwa kaleeb cikin babbar murya yace, Aje ajefawa zakuna ita su cinyeta da ranta akawo qashinta asa 'dakin kayan tarihin mineelik... Da ido adama dake dake gefensa tayiwa sultan aqeel magana ya gyara zamansa tareda kallon sauran sarakunan dake Royal hall din yace, Idan aka kashe wannan baiwa batareda ta fadi wainda suka sakataba baka kai qarshen matsalar a mineelik ba sbd gobe ko jibi magajin ne da kansa za'a kashe kuma hakan zaisakawa mutane wasi wasin hukuncinka tunda ta fadi wainda suka sakata anshare anyi kamar bata fadaba. Ido cikin ido yakalli sultan aqeel yace, Babu Wanda ya isa yayi wasi wasin hukuncina a qarqashin mulkina da ikona ko wanene batareda na ciyar da namansa ga dabbobinaba. Murmushin mulki sultan aqeel yasaki yace, Hakane kuma idan kanason hakan yacigaba da faruwa saika nunawa mineelik Kaine sultan kuma Kaine kake yanke hukunci kowane irine akan ko wanene. Nan take sauran sarakunan suka marawa gaskia baya suka qalubalanci sultan akan adalci idan har sultana ce tasakata to ayi adalci ayanke hukunci daidai yanda yakamata. Atake mutane suka fara kallon kallo da hayaniyar abinda aka fada nan mamaki ya kama sultan kenan har akwai wainda zasu iya tambayar hukuncinsa su qalubalanci yanayin mulkinsa Atake yace aje a kama Jakadiya arufe ya 'daga hukuncin zuwa gobe duk me hannu aciki kafin faduwar rana baya duniya. Lokacinda akaje aka kama Jakadiya aka rufe Sultana kuwa rufe sashenta akayi tareda aje masu tsaron qofar da doka mai qarfi daga sultan babu Wanda zai shiga gurinta ajira hukuncinsa zuwa gobe. Lokacinda zancen ya isa kunnen maheer kai tsaye gurin sultan yanufa akai masa iso lokacin anwatse sai gobe a shaida hukuncinda zai iya yankewa. Kallonsa yarima yayi cikeda takaici da baqin cikin yanda yasan sultana bazata aikata hakan ga yayansa ba amma ya yarda haryana iya tunanin yanke mata hukunci Kai tsaye yace, Amatsayina na uban magaji zan kar6i mulkin mineelik har lokacinda zai girma ya karbi da hannunsa. Wani irin murmushin takaici sultan yasaki batareda yakallesaba yace, Mulkin mineelik da za6ar mai mulkin na mutum 'dayane yanxu dan haka ka rasa damarka, Mahaifiyarka kuma koni bazan iya kubutarda itaba idan har bincike ya nuna da hannunta aciki. Yana fadar haka ya shige tabarsa zaune idanuwansa na kadawa jajir. Duk inda tashin hankali yake masarautar na ciki dan shi kansa sultan jinjina alamarin yake aransa yana jaddadawa yana kuma fatar bincike yasa kar asamu hannun sultana aciki. Acikin daren babu kalar azabar daba'a bawa mamaniba tace Jakadiya tasaka ta. Jakadiya aka hau bawa baqar azaba amma daqyar take iya furta babu saka hannunsu aciki. Acikin daren saqon neman sulhu da sassaucin hukunci yazo daga masarautar Libya dakuma wasu masarautun duk sai alamarin yasake girmama ya sake cabewa sultan gashi komene adaren ne sbd gobe dolene zai yanke hukunci. Nuratu datun jiya take kuka da tashin hankalin halinda mamani ta fada koda bincike yazo kanta ba qaramin rikicewa tayiba saidai tafada musu komai na dangane da zancen dasukaji su Jakadiya nayi da sultana itada rumanah akan basuso ta haifi namiji. Atake aka kaiwa sultan wannan zancen hankalinsa ya matuqar tashi saidai har lokacin yanada wasi wasin zancen ga asirinsu na 6oye daya fara shigowa cikin zancen Wanda tonuwar dolema yayi gaggawar yanke hukunci sbd kar maganar ta bankado atake ya yanke hukuncin kisa ga dukkaninsu ukun gobe. Acikin daren hankula suka masifar tashi jin anyekewasu sultana hukuncin kisa washe gari. Duk wata zuriar masarautar tun acikin daren suka fara isowa musamman 'yayan sultana da kuka sunyisa na zuci dana fili hankalinsu amatuqar tashe yake. Yarima maheer Kansa ya rufe adaki duk yanda yake tunanin masifar ta wuce nan abu 'daya yasani bazai mahaifiyarsa ta fuskanci hukuncin kisar wulaqanciba. Kwance take lamo idanuwanta jajir ko kukan bata iyayi duk abinda yake faruwa bata saniba sbd ta hana abar kowa shigowa gurinta. Ahankali taji antsaya akanta batareda tadagoba ta lumshe ido tareda budewa taji muryar suhailat cikin wani irin yanayi tace, Nazo neman alfarma agurin sbd kece kawai zaki iya tsayarda abinda ke shirin faruwa. Tashi zaune tayi ahankali batareda takalli suhailat dinba Itama suhailat sauke kanta tayi sbd batason kallon rumanah dan ganinta ke tuno mata da ba itace zuciyar mijintaba. Hawayene suka gangaro mata tasaka hannu ahankali tashare taci gaba da cewa, Nice uwar datai rashin abu biyu lokaci daya kuma zuciyata cike takeda neman adalci, Ina roqonki amatsayina na uwar data rasa 'da da mahaifarta akan adalci zanso ganin anmin adalci saidai bazanso akashe Wanda bashine mai laifinba sbd mai laifin zai cigaba da aikata 6anna aboye har wadda tafi wannan. Cikin dasashiyar murya da sanyi tace, Adalcin nima nake nema amatsiyana na marainiyar da aka raba da iyayenta dakuma uwar da aka rabata da 'danta tun bata gama warkewa daga zafin naqudarsaba. Asubar fari yashigo dakinta idanuwansa da yanayinsa suka karya mata zuciya ta dauke kai daga kallonsa tareda mayarda kanta kan gwiwoyinta. Tsayawa yayi agabanta zuciyarsa cikeda baqin cikin kasancewarsa shine zai roqi wani yabasa sarautarda shine ya gada saidai yasan kubutarda ammynsa na nufin ya karbi sarautar ayau yazamo shine zai yanke hukunci sbd yagano sultan sbd 6oye wani sirrinsa yakeson yanke hukuncin da gaggawa ayau. Kallonta yayi da idanuwansa dasukai jajir yace, Inason kibani sarautar mineelik ayau. Kallonsa tayi da sauri da jajayen idanuwanta dake budewa daqyar sbd kumburi. Juya mata baya yayi yace, Ki shirya ina jiranki kafin lokacin yanke hukuncin su ammy yayi. Ficewa yayi tabisa da kallo zuciyarta na harbawa. Cikin wani irin yanayi na sabon tashin hankali ta 'dauki abeel hassan ta fito palo takalli nuratu dake rakube tun acikin daren tana jiran fitowarta tayi kuka har batada qarfin yin wani. Kai tsaye tace, Meke faruwa? Da sauri nuratu ta tashi ta zube gabanta tana hawaye tace, Ina neman afuwa akan shaidar dana bayar akan sultana da jakadiya gashi zasu rasa ransa sanadin shaidata saidai wlh ina rantsuwa da rayuwata mamani bayin kantabane sakata akayi saidai wlh bansan wayake sakataba dana fada nan fitardasu sultana dan haka ashirye nake da daukar hukuncinki. Da wani irin sabon baqin ciki da takaici takalli nuratu saidai takasa cewa komai ta nufi qofa ta fice kai tsaye sashen suhailat ta nufa. Zaune take a dakinta taqurawa akwatinanta data saka Carolina hadawa ido idanuwanta jajir. Tsayawa gabanta rumanah tayi tareda miqa mata abeel hassan idanuwanta na cikowa da hawaye tace, Duk duniya ayanxu kece kawai na yarda dake akan 'dana sai Ammy dan haka ina riqonki daki riqesa har sai lokacinda kikaji zuciyarki ta gamsu da adalcin dazan baki, Na miki alqawarin duk Wanda yakeda hannu aciki ayau zai fuskanci hukuncinsa. Ficewa tayi kai tsaye ta nufi sashenta tashiga wanka zuciyarta na wani irin zafi tana fitowa tagansa tsaye cikin 'dakin idanuwansa jajir ya kalleta ta 'dauke kanta tareda isa gaban madubi ta zauna. Cikin zafi ya jawota gabansa cikin 'daga murya yace, Me kike nufi da abinda kika fadawa suhailat? Bata kallesaba tace, Kubutarda uwata. Sakinta yayi da sauri tareda kallon cikin idonta yace, Kinsan abinda kike fada? Kinsan abinda hakan ke nufi? Bana buqatar ki shiga komai abu 'daya nace kiyi shine ki bani matsayin danace inaso.... Kallonsa tayi da jajayen idanuwanta cikin rawar murya tace, Nima bana buqatar ka saka kanka cikin ha'dari dan haka bazan taba baka mulkin mineelik ba koda hakan na nufin rasa rayuwatane.... Riqota yayi da qarfi tareda girgizata yace, Idan kina sona bazaki taba bari ataba mahaifiyata ba sbd itace rayuwata dan haka dole zaki bani mulki. Hawayen dasuka cika mata idone suka gangaro mata ahankali tace, Namaka alqawarin babu abinda zai samu uwar data haifi halitta mafi soyuwa arayuwata kozan rasa raina. Shiga jikinsa tayi ahankali tareda rungumesa hawaye na tsinke mata. Rintse ido yayi tareda rungumeta ahankali ya furta, KECE RAYUWATA UMMU-RUMANAH BULAMA. Dagowa tayi takallesa hawaye far in ciki na tsiyayo mata saidai bazata iya cewa komaiba. Ruwan kan table din dake tsakiyar dakin ta dauka tareda kaiwa bakinsa tana tsiyayar hawayen tausayinsa dana kanta. Ahankali yasha yana kallon cikin idonta. Ahankali ta furta, Karka gujeni kome zanzama arayuwa dan allah, Ko bayan raina kayi kayi alqawarin tunawa dani. Lumshe ido yayi jikinsa na mutuwa idanuwansa na fara gani dishi dishi a firgice yake kallonta sbd gano wani abune tabashi saidai kafin yayi wani yunquri ya zube kan gadon ta durqusa ta gyara masa kwanciyarsa tareda shafa fuskarsa ta miqe. Dukkanin wani maison sheda hukuncin sultan na cikin qasar da wajenta sun hallara sultan na fitowa guri yayi tsit ya zauna kan kujerar mulkinsa atake aka fito da mamani da jakadiya dukkaninsu babu mai iya tsayuwa sbd azaba da 'daurin dake jikinsu. Kukan baqin ciki Jakadiya takeyi sbd irin mutuwar tozarcin dazasuyi tareda sultana. Mamani na ganin masu jiran umarni sun tsaya akansu da takobuna suna kashe ido sbd laifi da qyallinsu hankalinta yatashi tabude ido daqyar tanason magana kaleeb ya take mata kai. Ana jiran ana fitoda sultana cikin wani irin ama aka sanarda fitowar uwar magaji. Atake kowa yayi tsit sultan yayi saurin kallon qofar Tafito cikin wata irin doguwar ethiopiany royal gown red colour mai tsananin tsawo da adon black stones wuyanta da kanta na kyallin farin zinari kallo 'daya zakayi mata kasan tana cikin baqin ciki. Cikin wainda ke tareda ita Dan tsaron lafiyarta ta kalli gefen daya jiki na rawa ya fidda bayananta dake rubuce jikin fatar rubutu ya miqawa sarkin na'din sarautar mineelik. Budewa yayi tareda fara karanto da qarfin muryarsa yanda duka alummar dasuka halarci gurin zasuji. "" NI UMMU-RUMANAH BULAMA MATAR YARIMA MAHEER UWAR MAGAJIN MINEELIK AYAU KWANA 'DAYA DA NADIN SUNAN MAGAJIN MINEELIK NA SAUKE SULTAN ABDULSHAMS ABDALLAH DAGA MULKIN MINEELIK NA KARBA HAR ZUWA RANARDA 'DANA MAGAJI ABEEL HASSAN ZAI KARBI MULKI DA HANNUNSA..""" Tsit koina yayi sbd firgici da mamaki Sultan da adama kusan atare suka miqe tsaye tsabar firgici. Ammy da ake fitowa da ita kadan ya rage ta yanke jiki ta fadi sbd jiyo sanarwar. Jiki na rawa sarkin nadi tareda duk sauran sarakuna da wazirai suka miqe ta nufi kujerar mulkin mineelik gabanta da numfashinta na fita da sauri Sultan dayayi mutuwar tsaye ya zare hular mulkin ya miqawa sarkin gida atake aka dauko kayan rantsarwa aka rantsar da ita atake ta zauna kujerar mineelik aka saka mata hular. Lumshe jajayen idanuwanta tayi wani irin baqon yanayi mai qarfi na shigarta Wani irin qarfin zuciya da taurin zuciya taji yana shigarta tsawon lokaci ahaka duk anyi tsit anajiranta. Ahankali ta bude idanuwanta dasuka bushe nan take tagyara zama takalli inda sultan yake zaune yana kallonta cikin isa shima yanajiran jin nata hukuncin ta juyo takalli indasu mamani suke cikin daga murya tace, Akawo abinda mamani tafiso aduniya. Cikin gaggawa aka jawo nuratu aka durqusar tsakiyar gurin kai tsaye tace, Ku yankata agabanta uwarta idan bata fadi Wanda yasakataba cikin seconds uku. #mamuhgee. [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: _*TARAYYA*_ _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *35* Not edited *Asalin Labarin mineelik* Soyayya da cin Amana haɗi da Yaudara suka, kafa daular, asalin masifar ya fara ne, daga ranar laraba ga watan maris 1836. Mafarin rigimar daga mutane huɗune, jigogin masarautar, Musaman Sultan Jamal wanda shi ya haifar da kome.... Tafiya suke a gajiye ga dare ya fara rabawa, yunwa da kishirwa ya addabesu, dan haka suka yanke hukuncin da zaran sun sami, wani guri a can gaba zasu yada zango kasancewa sun fito daga yanki sham, fatauci duk cikinsu babu wanda yake iya magana sai Jamal, sabida Allah yayoshi mutune magananne, da kuma son raha, "Kayyasa! Ajani karda ka gaji da tafiyar dan naga kaman rakuminka ke janka ba kai kejanshi ba." "Wai shin Jamal baka gajiya da magane, haba tun da muka fito kaiɗai ke surutu gaskiya kacika surutu kayi mana hakuri haka dan yunwa muke ji." inji Kojo. "Shi kenan kojo nayi shiru kuma bazan sake magana ba, amma kusan matuƙar muka ce zamu shiga Ehtophiea a wannan daren akwai damuwa mu yada zango anan gaba." Shirun da sukayi ya tabbatar da amincewar sauran. Tafiya sukayi sosai har suka isa dajin kurfa, wanda yake cike da ababen tsoratarwa, ɗan tafiya kaɗan sukayi ɗayansu amari yaga wani irin Haske mai tsananin kyalli cikin duhu ya ware ido sosai yasake kallawa domin kuwa ya tabbatarda mage yake gani mai shegen hasken nan kamarna zinari cikin zaquwa da fargaba yace. "Ku dakata naga wani abu, kamar Zinari." "Amari nima nagani tsoron siffar abin yasani shiru gashi can kamar mage ko?" Inji Jamal, Linzamin rakumarsu suka ja, suka tsaya Jamal da Amari suka sauka, daga bisa rakumansu, Ajani da Koja suna tsaye suna kallonsu, tafiya sukayi me ɗan nisa suna niman Zinarin basu ganshi ba, Tsaki Ajani yayi wanda ya kasance shine babbansu, cikin fushi yace. "Dalla kuzo mutafi kusan inda muke ciki wannan dajin kurfa cike yake da al'ajabi da ban tsoro matumar kuka ce zaku bi na gane gane mutuwa zamuyi ku fito muje." Murmushi Amari yayi cikin nutsuwa yace. "Na rantse da abin bautana bazan bar dajin ba, Jamal idan zaka bisu ba damuwa amma ni sai naga abinda ya turewa buzu naɗi" Shiru sukayi sunsan Amari da kafiya da kuma taurin rai, matukar yace zai yi abu ba makawa sai ya aikata, Cikin laluma kojo yace. "Shikenan zamu tayaku nima! Ai duk cigabanmu ne, Ajani kayi hakuri mu tayasu niman zinariyar." Tsaki Ajani yayi sannan ya koma inda suka ajiye rakumansu, suka kafa tanti karan dake wajen dajin suka tsinta, suka kunna wuta suna shan ɗumi,( bawai dan lokacin sanyi ba'a mutanen da suka kuna wuta su zauna suna hira, musaman fatake matafiy idan suka yada zango.) Zama sukayi a gurin, sannan suka ciro guzirinsu suka fara ci, bushashiyar gasashiyar fulawa sai bushashen inabi, sai ruwa suna ci suna hira, har dare ya raba sannan kowa ya koma tantinsa. Kasancewa dajin mugun gurine koda suka shiga sai da suka kafe ilahirin gurin dan kar wani mugun dawa ya iya shigowa ya cutar dasu. Asalinsu wadanan, Fataken yan garin Ethiopia ne, sun kasance marayu basu da uba basu da Uwa, sai wani marikinsu wanda shima bai jima da mutuwa ba. Ajani shine babba a cikinsu sai mai binshi Kojo, sai kuma Amari da karamunsu jamal. Dukda kasancewarsu marayu haka bai hanasu kaunar junansu ba, dan ko ciwo ɗaya keyi duk sai sun kwanta kamar marasa lafiya, dukda haka suna da mabanbanta halaya, Ajani baida yawan magana, amna kwai saurin fusata sai amma haka bai sashi ya gaza zama mai hakuri ba, Sai Kojo, mutune mai matukar fahimta ga daɗin zama da kowa kuma duk inda zai zauna zai matukar wuya kaji ance ana rigima dashi, sabida ya iya zama da kowa, sai Amari, masifaffe mara hakuri amma kome zaiyi akan gaskiyarshi yake, yana da matukar taurin kai, dan shi duk abinda yasaka agaba toh sai yaga bayanshi, amma mutune mai me tsage gaskiya. Sai Autansu Jamal wanda ya kasance mutum ne hakuri da juriya ga barkwace da iya zama da mutane, kuma yana da shiga rai dan duk inda ya zauna sai kasamu ana alfahari dashi, sai dai yana da abun dariya dan idan yazauna kusada kai sai ya cika maka cikinka da barkwace da raha. Wannan kenan.... Washi gari da safe duk suka tashi, nan suka karya a gurguje suka shiga dajin, niman zinarin nan, har rana takusan faɗi basu gani ba, tsurawa dajin ido amari yayi yace. "Jamal jiya ba'a nan muka ga kyalin zinarin mai sufar mage." Gyaɗa mishi kai Jamal yayi cike da bashi kwarin gwiwa, murmushi Ajani yayi sannan yace "Amari zan tura kojo gari ya sayo mana kayan aiki sai mun tono wannan zinarin na yarda da kai." Cikin farin ciki Amari ya rungume Ajani yana cewa, Yene dan uwa. Gurin tantinsu suka dawo suka ciro kuɗi silalar akabawa Kojo, yaje ya sayo kayan aiki. Tafiya ce ta wuni guda dan haka ya haye rakuminshi ya kutsa cikin gari, bai isa ba sai da duhu ya fara rabawa, sannan ya isa gidansu anan ya kwana washi gari ya shiga kasuwa ya sayi abinda suke bukata wanda, na kayan tono, Yana gamawa ya aza kayan akan rakuminshi,sannan yabar garin, Tafiyar kaman dai yanda yazone sai da dare ya fara ya isa gurinsu dan ba iyakar kayan aikin yasaya ba, har da kayan abinci yasaya musu, Zama sukayi a gurin suka ci abinda ya kawo, sannan suka shiga hira yanda zasu tono rijiyar zinarin. Suna gurin har dare ya farayi sannan suka shige tantinsu. **** Washi gari suka je inda suka hango zinarin suka shiga tonoda kwashe kasa, a hankali suka ta aikin tono har dai sukayi nisan zango ga dare yayi dole suka hakura zuwa gobe. Washi gari ma haka suka cigaba da tonon ba dare ba rana har sai da suka shafe kwanaki goma sha takwas da yini daya babu zinarin babu labarinshi karshe hakura sukayi da tono, duk suka zauna jigum, cike da bakin ciki Amari ya fashe da kuka, wanda ya kashe jikin yan uwanshi, rarrashinsa suka shiga yi, kafin yayi shiru mikewa yayi yace. "Dole sai na isa ga, Ebo sarkin bokaye dan shine zai iya duba min abinda idanuna ya gani." Cikin son mara mishi baya suka mike take suka nufi cikin gari, dukda dare ne haka bai hanasu tafiya ba, har suka shiga garin gidansu suka nufa, suka kwana washi gari suka tashi dukkansu suka nufi gidan Ebo. Sarkin bokayen garin, tun daga bakin kofar gidanshi suka hangoshi kwarjale, irin wanda mahajata ke raɓawa akafaɗarshi hannunshi rike da sandar tsafi, goshinsa yashafa bakin gari, inda yaja jan gari a goshinsa, "Lalle lallae da zuwan sarakunan karnin farko, barka da zuwanku, a koda yaushe k'addara kamar zare ce mai kaifi, amma shahara da ɗaukaka tana biye a bayanta ku shigo ciki." Jikinsune yayi sanyi, zama sukayi akan fatar zakin dake shimfiɗe, a tsakar ɗakin, shi kuma ya koma kan kujeranshi. "Ina jinku." Yace musu, tunda suka ɗauko niyyar zuwa gurinshi, yaji haka ajikinshi sai dai lokacin da ya hangosu yaga tagomashin ɗaukaka wanda yake ɗauke da duhun na ban mamaki. Cikin zakuwa Amari ya buɗe bakinshi zaice wani abu m, take bokan ya dakatar dashi ya kalli Ajani, ya masa alamun yayi magana. Cikin nutsuwa ya faɗa mishi abinda suka gani. D'auko wata yar jaka yayi, ya buɗe bakinta, ita wannan jakar da fatar jimina akayita, sabida ajiyar abubuwa kananu. Wasu duwatsune a ciki wanda suke cakuɗe da wuri, wasu kalamai bokan yayi sannan ya jijjiga duwatsun ya watsa, a tsorace yakalle su baki ɗaya sake ɗiba yayi ya watsa, a firgice ya mike yace. "Shin kungatane?" Suma atsorace suka kalli juna, sannan suka kalleshi, kaman haɗin baki suka ce. "Wa kake nufi?" Komawa gurin zamanshi yayi a nutse, yace. "Sarauniya Mineerlik?" "Mineerlik kuma? Sarauniya kuma ai mu bamu ganta ba, kawai mage muka gani ita kuma ta zinarice." Suka faɗa mishi haka a tsorace. "Tabbas ita kuka gani, itace tafito dan sau ɗaya take fitowa ashekara, kuma ta tafi bazaku sake ganinta ba sai wata shekara idan da rabon haka kuma ko wace shekara da kalar siffar datake fitowa amma tabbas k'addaranku ce takaiku gurin har kuka ganta." Shiru sukayi cike da damuwa, suka shiga kallon juna Kojo shi yayi karfin halin tambayar bokan yace "Wacece ita haka.?" "A'a ɗan saurayi wannan duniyace ta taskar arziki, daula ce ta musaman Sarauniya Mineerlik sunanta sunan kujeranta." "Toh Ebo taya zamu sake ganinta? Tunda ake kaddaranmu ce ta haɗamu da ita domin kuwa wannan zinarin saimun mun mallakesa" Inji Ajani, Gyara zama yayi cikin yarda da abinda zaice. "Wato wannan dajin da kuke gani ba daji bane, kamar sauran da dazuzzuka, shi ɗin alkarya ce ta aljanu ko nace muku duniyar aljanu ce, shi yasa yake cike da abubuwan al'ajabi, masana tarihi sun tabbatar da cewa, babbar masarautane a gurin me ɗauke da babbar fada na sarkin aljanu Penya, shine mamallakin fadar da kuma alummarsu ta aljanu, lokacin da cutan ajali yazowa penya sai ya bar wasiya, koda ya mutum Kalsh shine shine magajinshi, alakacin matar Kalsh Sultana Neelah tana ɗauke da tsohon cikin, haihuwa ko yau ko gobe.... Bayan kwana biyu jikin mai martaba penya yayi tsamari, haka duk wasu likitotin gargaji suna fama dashi, tashin hankali yayiwa Kalsh yawa domin a lokacin aka sanar mishi, Sultana Neelah tana, kan gwiwa, Hankalinshi yayi matukar tashi, ana cikin haka Sarki Penya ya mutu, hankalin Kalsh yayi matukar tashi ga rashin Uba ga matar a wani hali gabi ɗaya sai ya shiga kiɗima, ana hidima kai mahaifinshi amna shi ya koma kofar ɗakin karɓan haihuwa, ya zauna. Sai da Neelah tashafe kwana biyar sannan ta sami nasaran haihuwar Y'arta mace, mai tsananin kyau wacce tunda ake haihuwa azuri'ar ba'a taɓa samun y'a kamar yarinyar ba, sai dai abin takaici kwanar Sultana Neelah ta mutu sakamakon ciwon cikin haihuwa, gashi a ranar aka bawa Kalsh mulkin garin, ga murna ga bakinciki, fito mishi da Yarinyar jakadiya tayi ta zube a kasa cikin kuka tace. "Sultan ga yarinyar nan, ta rasa uwarta a daren jiya." Idanunshi cike da zubda kwalla ya karɓi Yarinyar ya ɗagata ga Alummarshi yace. "Sultan Kalshe Penya, Nasamu Y'a mace naka mata Suna Mineerlik, haka kuma kujeran mulkina shima sunansa kenan Mineerlik, da fatan ku sanya mata albarka." Cikin maɗaukakkiyar murya alummar aljanu sukace mun ji mun amince da abinda kace munawa Sultana Mineerlik, Barka da zuwa da kuma albarka ya cika rayuwarta." Juyawa Sultan kalsh yayi rike da jaririyar, zuwa cikin gida ya isa har ɗakin da gawar Sultana Neelah, yana shiga ya zuɓa gwiwarshi cike da zubda kwallah yace. "Neelah kin ɗaukar min alkawari baki cika ba, Ina soyayyar da kika fada min zamu shimfiɗa ina kaunar da kika min alkawarin zamu nunawa abin ciknki Neelah ya zaki tafi kibarni da ɗawainiyarta, Ina soyayyar da kika min alkawari min, abar kaunata kin tafi kin barni da kewarki da soyayyarki wanda yake tankar gubace a gareni." Kuka yake cike da damuwa da ɗimauta, ruwan kwallar dake zuba daga idanunshi yana sauka akan fuskar mineerlik, a hankali ta buɗe idanunta tana kallon mahaifinta, sai ta rufe, sabida ɗigar kwalla, jakadiya ce tazo amshi Sultana Mineerlik a hannunshi wacce take motsi da kuka kasa kasa, na alamun yunwa, dan har tasaka hannunta abakinta.... #mamuhgee [7/29, 9:29 PM] Hauwa'u inna: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *34* Not edited. Arazane sultan,adama,ammy,da baqin sarakunan dasukazo suka kalleta Babu Wanda ta kalla acikinsu tayiwa kaleeb kallo 'daya idanuwanta na sake bushewa cikin gaggawar cika umarninta kaleeb ya daga shar6ebiyar takobinsa mai cire kai lokaci 'daya ya 'dora a wuyan nuratu dake hawaye ta qurawa rumanah ido. Numfashin wahala mamani ta fitar cikin tashin hankali ta bude baki zatai magana adama datai mutuwar zaune tayi sairi tashi tsaye jikinta na wata irin tsuma zatai magana rumanah ta 'daga hannu batareda takalleta tace, Duk Wanda yayi magana batareda hukunci ya gama tabbatuwaba abakin rayuwarsu ko wanene. A gigice adama tasake kallonta cikin wani sabon tashin hankalin takoma ta zauna zufa na karyo mata jikinta na wata irin tsuma. Tayar da ita akayi tana numfashin azaba takalli takobin datake qyalli a wuyan nuratu takuma tabbarda yankata din za'ayi. Ahankali rumanah ta 'dagawa kaleeb kai alamar yacika aiki. Atake ya 'daga takobin cikin wahalalliyar murya mamani tace, Gimbiya adama ce. Cak kaleeb ya tsaya sbd harya 'dora takobin a wuyan nuratu harma saida ya'dan yanketa. Arazace sultan yakalli adama data jiqe jagaf da zufa jikinta na tsuma tanason kare kanta gashi ance duk Wanda yayi magana bbakin ransa kuma tasan tsaf rumanah zata iya sbd tasan abinda ka cikin karagar zaifi shigarta kasancewarta mace dan haka zatafi rashin tausayi da imani. Sarakunan dake gurin duk ita suke kallo cikin mamaki yayanta kuwa kuka suka fashe dashi gashi babu ikon ko qwaqwaran motsi. Rufe ido rumanah tayi wani irin yanayi na tsuma zuciyarta gawar 'danta da iyayenta tana mata yawo ido da irin tozarcinda ammy ta fuskanta akan hakan Fuskar maheer ce ta fado mata da irin tashin hankalinda tagani ataredashi tsakanin jiya zuwa yau ta bude idanuwanta dasukai jajir tace, Ni sarauniya ummu-rumanah bulama na halastawa takobin kaleeb adana jinin adama kisheer ayau agaban mijinta da 'yayanta tareda sauran alumma duk Wanda ko a fuska ya nuna hukuncina baimasaba a shayar dashi dafi daidai irin Wanda adama tashayarda qannen magajin mineelik., Baiwa mamani arufeta mai rubuta tarihi yaje tabasa tarihin sarauniya rumanah arubuta atarihin mineelik tana gamawa bazata qara minti biyar aduniyaba a shayar da ita Kofi 'daya na daafin macijin dayafi kowanne kaifin dafi, Sultana zaarah da jakadiya sunfita da zargin da ake musu. Sultan abdulshams arufesa a turakarsa babu shiga babu fita aabisaga zarginsa na qoqarin yanke hukunci batareda bincikeba harsai angama bincike akan niyarsa sultana zaarah ce kawai keda damar shiga da fita agurinsa sai yarima maheer. Arikice sultan yakalleta ransa na mummunan 6aci da baqin ciki ace rana 'daya cikin mintunan dabasu wuce biyarba baiwa wadda bama asalin 'yar qasaba ta saukesa akan mulkin daya gada iyaye da kakanni, Ta yankewa matarsa kisan wulaqanci agaban dubban jama'ar dasuke shakkar ko kallon inda yake sannan yanxu tace arufesa a turakarsa wannan shine tozarci mafi muni arayuwa... Yanxu ta karbi mulki idan tagano shine asalin dalilin mutuwar iyayenta akwai masifa sosai sbd yanda sihirin karagar nan ke shigarta nan cikin qanqanin lokaci zata zamewa kowa masifa mai matuqar hadari musamman shi saidai duk masifa duk balai bazai bari yayi mutuwar wulaqanci a hannuntaba koda hakan na nufin hada hannu da balain da aka binne shekaru tun kafinsu. Kama adama akayi aka fara janta tayi saurin kwacewa ta isa gaban rumanah ta zube tana kukan tashin hankali jikinta na mugun karkarwa saidai takasa magana sbd umarninda rumanar tabayar ko kallonta rumanah batayiba ta kalli su kaleeb atake suka fara yiwa adama jan wulaqanci. Jikin ammy ne yadauki rawa cikin sabon tashin hankali take kallon rumanah tana girgiza kai sbd matuqar tafara mulkinta ayau da zubarda jinin wani to tabbas zaiyi wuya bata zamewa mutane abin tsorobas. Qoqarin isa gurin rumanah din tayi aka dakatar da ita ta hanyar tareta tayi saurin kallon rumanah data rufe idonta tanajin wani irin baqon yanayi shigarta. Cikeda rashin imani da tausayi kaleeb ya daga takobinsa yacire kan adama data mutu tana ihu da fizge fizge. Tsit gurin yayi sbd tsoro da firgici sbd duk mulkin sultan ba'a taba kashe mutum agaban alumma ba sai yanzu nantake kowa yaji tsoro da fargaba tareda tashin hankali na shigarsa atake kaleeb ya 'daga takobinsa dake 'digar jinin adama sama ta bude idanuwanta ahankali takalli jinin dake diga qasa ahankali tasauke ajiyar zuciya ta miqe tsaye. Cikin wani sauti da babban sauti sarkin na'di yace, Dogon zamani MINEELIK ASSULTANA UMMU-RUMANAH UWAR MAGAJI. Juyawa tayi wasu irin samudawan masu bata tsaro da kuyankinta mata suka mara mata baya tashige. Tafiya kadan tayi ta tsaya cak sbd abinda takeji ajikinta Wani irin abu takeji kamar yana tafiya da motsi ajikinta ta dafe qirjinta da takejin yana quna. Ammy tayi saurin nufota aka sake tareda Rumanar ta 'daga musu hannu daqyar alamar subarta ammyn tayi saurin qarasowa kafin tayi yunqurin ta6ata sukaga ta yanke jiki ta fadi jini na fita ta hancinta atake hankalinsu yayi masifar tashi ammy na qoqarin 'dagota suka gansa kansu idanuwansa jajir jijiyoyin sun firfito ya durqusa ya dauketa ya nufi sashenta da ita cikin qanqanin lokaci aka zuba wasu irin tsaro tundaga qofar sashenta har zuwa qofar masarautar atake labarin halinda take ciki ya yadu nan mutane suka sake shan jinin jikinsu atake aka rufe duk wata qofar shige da fice dake mineelik aka dauko duk masu bada maganin sarauta na asalin gargajiyarsu nanda nan aka hau dubata suna qoqarin tabbatarda abinda suke tunani. Cikin wani irin tashin hankali da damuwa yake, Zafi sosai yakeji acikin xuciyarsu akaro na farko dayaji zuciyarsa na karaya akan abu saidai yasan mutuwace kawai zata rabasa da rumanah dan haka duk abinda zata zama ayanxu ashirye yake daya sadaukar da rayuwarsa akan cetota daga masifar dake tattare da wannan karagar. Jini ne sosai yake fita ta hancinta ahankali tafara wata irin jijjiga jijiyoyin jikinta suka ringa firfitowa Kore sosai nan take hankalin su negasi(masu maganin gargajiyar qarnin baya na sarauta) ya tashi Maheer da idanuwansa sukai mugun rikidewa yayi saurin nufarta zai rungumota cikin wani irin sauti negasi yace, Karka kusanci inda take ko kusa a wannan yanayin hadarine mai matuqar gaske dankuwa dafine yake yawo ajikinta yanxu idan jininta yafi qarfin dafin zataci qarfinsa ta tashi idan kuma dafin karagar yafi qarfin jininta shikenan sai hakuri sbd har abada bazata koma daidaiba zata zama rabi hankali rabi nakashe. Cikin wani mumman tashin hankali ya dafe goshinsa akaro na farko yaji idanuwansa suna qoqarin tara hawaye ya fito dakin baya gani sosai sbd tashin hankali Ahankali yaji andafasa yana juyowa yaga suhailat rungume da abeel baisan sanda ya fada jikintaba ta rungumesu gaba daya shida abeel din hawaye na gangaro mata cikeda tausayinsa dana rumanah taso tafiyarta ayau saidai ganinsa Cikin halinda bata taba ganinsaba yasata jin bazata iya tafiya tabarsa a lokacinda yafi buqatarta,tabbas idan tanada wata qaddara arayuwa to soyayyar maheer ce dan haka kamar yanda zai sadaukar da rayuwarsa gurin kulada rumanah duk halinda zata shiga mai kyau ko mara kyau to itama zata zauna ta sadaukar da rayuwarta gurin kula dashi da zame masa garkuwa duk lokacinda zai nemi hakan. Ammy dake zaune tareda sauran 'yayanta yayun yarima sun biyu da Jakadiya da sauran masu tsaro da jiran tsammanin halinda ake ciki ta rafka tagumi zuciyarta na harbawa da qarfi sbd tasan me hakan ke nufi dan kuwa rumanarsu tariga ta tafi sbd idan har komai yagama shiga jikinta duk abinda yafaru shekara da shekaru tun kafa mineelik zata gani Wanda shine idan kaga masifun dake ciki yakeda wuya baka haukaceba idan ka farka. ASALIN MINEELIK....... #mamuhgee Kuyi manage na fitane so mu kama gobe. [7/30, 6:33 AM] ummul aulad: *_TARAYYA_* _wattpad@mmamuhgee_ _Haske writers association💡_ *36* _Not edited_ _A gaggauce_ Mineelik nada kwarjini da wani irin haske na tsananin kyawu Wanda yasaka Sam babu mai ganinta daga haifinta sai mai kulada ita shiyasa bakowane yasantaba musamman daya zamto itace kujerar mulkin mineelik ayanda abin yake mahaifinta yariga yayi amfani da wani irin sihiri akan karagar da sunan mineelik yanda ko bayan mutuwarsa babu Wanda zai iya raba mineelik da karagarta kuma barinta a nahiyar na nufin mutuwar duk Wanda ke nahiyar kuma babu Wanda yasan da hakan sai ita mineelik din da mahaifinta sbd ganin bai haifi namiji ba yasa aka fara farautar karagar mulkin. Mineelik na zama cikakkiyar budurwa qannan mahaifinta su hudu suka hada kai suka kashe mahaifinta mutuwar wulaqanci sbd wani irin zalamar son hayewa karagar saidai bayan kashesa suka kashe junansu agurin sbd kowa nason shine zai hau. Lokacinda mahaifin mineelik zai mutu saida ya shafawa karagar jininsa dake zuba na suka hudu dasukai masa cikin tsananin azaba da taurin zuciya tareda fushi mai tsanani ya daf karagar yace, Ni penya maqagin wannan karagar ayau jinina ya zuba sbd wannan dazata zamewa duk wani makusanci agareta masifa  ayau ina mata baki mai hadeda tsinuwa duk Wanda zai hauta tazamo ajali mai masifa agaresa matuqar ba MINEELIK-ASSULTANAH bace take kanta har ranar dazata na'da wani akai da kanta sbd jinina da aka zubar akanta daga wannan qarni nawa ta haramta ga dukkanin qarni masu zuwa. Lokacinda mineelik ta fito bayan mutuwar mahaifinta aranar duk Wanda ke bousk yaganta sukaga zallar kyawun halittar dabasu taba ganiba saidai cikin rashin sa'a fitowarta tasaka rayuka da dama mutuwa dan kuwa wani irin haskene da maganadisu atareda ita dake jan mutane zuwa gareta Wanda wannan abin shine atareda karagar mai janyo mutane da rufewar zuci da ido akan hawanta. Ranarda mineelik tahau karagarta amatsayin assultana aranar akayi wani irin tashin daya faru aranar shine koda gari ya waye duk Wanda ke nahiyar babusa. Tashin hankali data shiga shine tabarwa datayi alamun mulkintane bazaiyi kyawuba sbd karagar tayiwa jininta qarfi kasancewarta mace. Ita kadai tayi rayuwa mai tsayi,shekaru masu tsayi batareda kowaba, Kadaici,qunci,baqin ciki da kewa sune abokanan rayuwarta sai karagar wadda ahankali take zuqe mata tausayinta sbd babu wani Wanda za'a yankewa hukunci a zubarda jininsa shiyasa abin yake cinta itakadai makari 'dayane mahaifinta yasanarda ita na wannan karaga shine soyayya mafi qarfi amma idan idan sadaukarwar abu mafi soyuwa tashigo. Sanin kaf acikin duniyarta babu Wanda zai iya ko 'dago kai yakalleta sbd kwarjininta bare ya iya samun soyayyarta saidai ta tabbatarda wannan azarbabin da  gaggawar tareda rashin tsoro da kwadayin sai bil adama. Wannan shine burin Hakan yasa ta rufe daularta babu  wanda yake ganinta sai ita tafara fitowa duniyar bil adama domin kuwa babu abinda take buqata da tsananin buri kamar soyayyar da babu irinta a qarnin. Aduk shekara da kalar suffan datake fitowa saidai bata taba dacewaba amma alqawarine bazata daina neman soyayyaba harsai ta mutu.       Shiru sukayi dukkansu kowanne najin zuciyarsa a bushe babu wani tsoro ko fargaba sbd dama nema suka fita duniya dan haka su sunga zinari kuma bazasu danganaba harsaisun mallaki wannan karaga Ajani ne ya gyara zama yayi gyaran murya yace, "Toh shi zinarin yana tare da ita kenan?         Gyara zama aqoob yayi cikin muryan da ta manyanta da tabbarda abinda zai fada yace, "Ita da kanta itace zinarin sbd itace kujerar mulkinta,sunanta sunan karagarta daularta itace arziki da kowa ke fatar samu saidai hadarin dayayi Katanga wa arzikin shine soyayyarta wadda itakaice mukulli ga wannan taskar arzikin.               Kallon kallo suka shiga yiwa junansu saidai babu Wanda alamar tsoro ko fargaba yake ataredashi Jamal ya kalli cikin idon aqoob yace,           Shirye muke da mallakar wannan dukiyar kota halin yaya koda soyayyar tatace mun shirya nema.       Murmushi bokan yayi yana jinjina qarfin zuciya da buried tareda rudu irin nasu sannan yace, "D'ayanku zai faɗa soyayya da ita amma kafin nan sai kunyi jiran  shekara ɗaya, wanda haka zai kasance kamar ganganci da wasa da rayuwarkune sbd hadarin dajin dakuma tsawon lokacin dakuma mataki uku masu matuqar hadari, idan kuka tsallake mataki uku da zai faru kafin bayyanarta toh tabbas soyayyar  ɗayanku zai kulu da ita, sai dai ba soyayyar bace mai muhimmanci dukiyarce mai mahimmanci domin sonda zai gwada mata shi zai sanyanta buɗe mishi alkaryanta da taskar mineelik.        Kallon juna suka sakeyi kowannensu idanuwansa acikeda rashin tsoro ajani yace, "Toh boka matakai uku da zamu bi dan samun kusanci da ita menene fa'idar haka."?   Mikewa bokan yayi tsaye, ya shiga zagayesu har ya tsaya a tsakiyarsu murmushi yayi yace, Zakusansu da sharadin taskar arzikin tamuce muduka.        Kallonsa sukayi cike da mamaki da jinjina kwadayinsa saidai zasu iya yin komai da mallakar taskar  kojo ya kallesa  yace, "Mun amince, zamu raba da kai. Dariyar  jin dadi yayi yace, Tareda yarana biyu za'ayi wannan tafiyar tareda rubuta sheda a faifan fatar raqumi da jinin dukkaninmu za'ai rubutun kowa zaibada nashi arubuta a ajiye tarihi ya shaida wannan taskar arzikin mineelik tamuce mu duka.             Babu musu kowanne yafitarda 'yar qaramar wuqarsa dake some a qafafunsu suka 'diga jininsu a 'yar qwarya akai rubutun atake ya ratayesa a bangon dakin. Yaransa biyu suka shigo yonas da haji yakallesu yace, Gasunan kuma tabbas akwai haske mai disashe duhu akwai duhu mai disashe haske.             Dayake zuciyoyinsu a shirye suke sun kafe kwaɗayi da son zuciya ya rufe musu ido ba tare da wani bata lokaciba suka amince Jamal dake gyara zaman wuqaqensa dake shanye da dafi kala dabam dabam na macijai da kunamu harma da dafin kada yace, "Tunda nine zan fara aikin kwada soyayyata dole kasona yazamo mafi nauyi a raqumi.             "Jamal kasonka shine mafi nauyi a raqumi sbd kaine zaka bamu gudunmawa mafi girma a cikin tafiyar, abinda zai faru idan kuka isa dajin domin jiranta akwai tsoratarwa daga muyagun aljanu da dabbobi masu firgitarwa da suke yawo cikin dajin,         matakin farko zai farane daga kwanaki uku kafin bayyanarta zaku kasance kamar makiyan juna a ranar farko, Zakiji tsana da qarfin son kashe juna mai qarfi na shigarku saidai karku bari hakan yaci qarfinku sbd dayafi qarfinku zaku kashe junanku cikin rashin imani. rana na biyu kuwa bazaku ga giftawar tsuntsaye ko wata dabba ko dayaba ko wni iri har kukan namun dajin bazaku ji ba. a rana na uku da zata bayyana wani mugun zafi da kishirwa zai buwayeku kamar zaku mutu, domin zaku ji har cikin jikinku zai koma kamar babu ruwa da jini a ciki, zuwa yamma ko dare zata bayyana, kai Jamal aikinkane kutsa kai cikin dajin domin haɗuwa da ita duk rintsi duk tsanani babu waiwaya.                     Shiru sukayi cike da al'ajabi suke kallon kallo sabida jin abinda zai faru dasu wanda suke gani kamar faɗar bokane,             Kallon bokan jamal yayi cikin nutsuwa yace. "Wannan indai shine sharuɗan mun amince.          Murmushi boka yayi sannan yace, Tafiyace mai zuwa babu tabbacin dawowa abin bautarku ya kubutar daku.            "Toh ni dai har yanzun abinda nakeson ji shine me zamu mata musamu dauko dukiyar mu mallaketa" Inji Amari.           Kallon Jamal bokan yayi cikin murmushi ba shi yayi tambayar ba amma ya maida idanunshi kan jamal, ɗaukar duwatsunshi yayi ya watsa har lokacin idanunshi nakan jamal,  juyawa yayi yace, "Lokacine zai nuna mana abinda zai faru ynz zan baku wasu madaurin dantse ku ɗaura gudun karku cutar da kanku. "Wannan zai kareku daga cutar da juna, sannan babu wani abinda zai cutarku nagama daku sai ranar da yasamu nasaran isa birnin Sarauniya mineelik, zamu karasa aikinmu nakarshe."      Mikewa sukayi baki ɗaya suka fita koda suka isa bakin kofa, kallon jamal yayi cike da tausayi, sannan yace. "Duk bayan lokaci mai dan tsayi ina son Babbanku yazo ya faɗa min cigaban da kuke samu." Kallon 'yayansa yayi ya jinjina kai cikin muryar jarumta da bankwana yace, Abin bauta yasa musake haduwa.      Haka sukayi bankwana dashi suka tafi.               ****   Tunda suka tafi, kaman yanda bokan ya faɗa musu haka ya faru, sabida sun ɗaura ɗanbar wani kudiri a ransu, ranar farko, suna kwance sai suka fara jin shashekar kuka, kamar na yaro kaman na babba haka aka cigaba da razanasu da wani irin mahaukacin kuka, kafin aka samusu dariya irin na bantsoron nan, can da dare yayi tsakiya, sai kana kwance a cikn tantinka za'a zo ana kiranka daga kan ajani aka fara, yana kwance ya dunkukune a marufinshi yaji an tsaya abakin tantinsa ana cewa. "Ajaniiiiiiiiiii"        D'auke numfashinsa yayi cak, tsabar tsoron, haka aka kewayasu ana razanasu.             Wasa wasa sai da suka kwashi fiyye da wata biyar ana tsoratasu da abubuwa a gurin tuni suka saba da rayuwa adajin sbd dama dukkaninsu sunsaba da rayuwa a daji dan haka yanzu gida suka dauki dajin sbd burinsu abune dazasu iya komai akansa. lokacin da suka cika wata shida Ajani yaje ya faɗawa boka abinda ya faru, nan ya zauna ya faɗa mishi abinda zasuwa Mineelik dazaran ta faɗa soyayya da Jamal. Bokan ya cigaba da cewa, " Matuƙar mukace muna son dukiyar baxata bamu cikin lumana ba. Karshe rabaku xatayi da ɗan uwanku amma idan mukayi haka toh babu wata damuwa sannan zan nema muku abubuwan da zakuyi amfani dashi, karka bari ɗan uwanka yaji labarin dan matukar yaji bazai yarda yayi aikin ba."       Gyaɗa kai ajani yayi sannan yabar garin ya koma dajin, nan suka cigaba da zama ga tsoratasu da ake ga kwanakin kamar baya tafiya, duk sun kaqu da faruwan haka,     Da zaran sun zauna hiransu kenan, akan yanda zasu juya dukiyarsu da suka samu, daga gareta, a hankali lokacin yana tafiya wasa wasa sai gashi har saura kwanaki bakwai zata bayyana,    ......        Bayan kwana huɗu wata rana da safe suka tashi da mugun faɗa kaman zasu kashe junarsu, kaman dai yanda bokan ya faɗa musu, karshe rabuwa dasu Jamal yayi ya koma gefe dan ya hassaso wannan rigimar yana cikin alamomin bayyanarta nan yatunatar dasu nan kowa yayi nesa da 'dan uwansa suna fidda wani irin gumi najin wani irin qarfi mai razanarwa na son kashe dan uwansa. rana tabiyu kuwa sun tashi da babu giftawar tsuntsaye ko ɗaya tareda wani irin tsoro mai firgitarwa dayake shigarsu wanda suka tabbarda natane amma haka suka dinga daurewa cikin wata irin jarumta.         Rana mafi tashin hankali shine ranar bayyanarta tsananin zafin da ake yaja sukaita fad'uwa, gashi sun shanye ruwansu, dakyar Jamal ya mike yace. "Yaku Y'an uwana wannan itace rana mafi hadari ageremu saidai ina fatar mana samun nasara." Daqyar su kojo suka rarrafo gurinsa suka rungume juna cikeda tsoron rabuwa da juna saidai burinsu ya zarce komai. Daqyar suka rabu da juna yana rangaji yana faduwa yana tashi sbd yunwa,zafi da qishirwa dake neman lahantasu ya nausa dajin inda ranar suka fara ganinta baisan inama yake jefa qafafunsa ba sbd azabar dayake ji cikin hanjinsa da cikinsa.  Duhun dare nayi yana isa gurin saidai ba'a cikin hayyacinsa ba sbd tuni yafara ficewa hayyacinsa atake ya yanke jiki gurin yafadi yana fitarda numfashi daqyar.     Ahankali kunnuwansa suka fara jiyo amo da sautin sarqar zinarin qafarta sanye take cikin kaya ruwan makuba fuskarta na fitarda wani irin annuri duk da cikin duhune atake yaji wani sanyi na yaye masa yunwa da wahalarsa suna barinsa ahankali.    Cikin wani irin takun nutsuwa da wata irin haiba ta nufo hanyar taku kadan tayi ta tsaya cak tareda lumshe fararen kyawawan idanuwanta. A hankali ta juyar da kanta tahangosa kwance ba alamar yana numfashi. A hankali takalli jikinta ahankali ta rikide ta sauya zuwa wata kyakkyawar bafulatar baqar Ethiopia sarqoqin jikinta na zinari suka koma duwatsun dandaye masu qaramin kyau ta nufosa numfashinta na wani irin sarqewa sbd wannan shine karo na farko data taba ganin wani biladama wadda take tabbarda shine Wanda ta dibi shekaru da qarnika tana jira. A hankali ta durqusa gabansa tareda daga daga dogon hannunta ta ta6a goshinsa atake ya bude idanuwansa yana kallon fuskarta bai san lokacin da ya sume ba, ruwan dake cikin goranta ta fulanin daji ta ɗauka ta watsa mishi, a hankali ya buɗe idanunshi sai akan fuskarta.         Cikin idanunta ya kalla kamar wanda aka ɗiga mishi ruwan gold, lumshe idanunshi yayi.     "Sannun ko" tace mishi... Wani irin sauti yaji daga muryarta wanda yakusan sake sumar dashi yayi wani irin jarumtar daidaita numfashinsa da nutsuwarsa yayi kalar wanda ke cikin tsananin wuya ya daga mata kai daqyar alamar amsawa yana jan numfashin qarya daqyar. Kasa wata maganar tayi tasauke kai tana kallon qafafunsa dake cikin takarmin fatar damisa.            Sunkuyar da kanshi yayi ahankali kwalla na zuba daga idanunshi cikin muryar tsananin damuwa da baqin ciki rayuwa yace. "Me yasa kika taimakeni? me yasa baki barni na mutu ba?  na gaji da rayuwar duniya gwara na mutu nabar duniyar nan."               Kallonsa tayi cikin sauri da nutsuwa da laushin murya tace, "Koma Ya-yane dai rayuwarka tana da amfani, ka daina cire tsamani da rayuwa, dan ko badaɗe ko bajima zaka amfani rayuwarka tana da amfani."                Kuka ya fashe da shi yans kwaɗa kanshi da bishiya yana cewa, "Kaicon rayuwa dan ina maraya shine bazanyi rayuwa kamar kowa, gwara mutuwata." Duk ya jiwa kanshi ciwo, tausayinshine da mamakin bil adamane ya kamata musamman ace yaganta mace cikin wannan dajin da tsakar dare amma bai nuna shakku ko tsoro da fargaba ba kodai yasan da fitowartane? Satar kallonta yayi yaga alamar tunani da nazarinsa takeyi yasan dole yayi dubarar hanata zarginsa hadiye wani mugun yawu tareda zabura gefe jikinsa na wani irin mazari ya nunata da hannunsa dake mugun rawa a tsorace da rawar murya yace, Ke...keee...ke wacece? Me...mee kikeyi anan ke daya? Kallonsa tayi ahankali cikin nutsuwa ganin yanda yarude yake neman zaucewa atake tasaki numfashi mai Sanyi tasaki murmushin daya sakasa zubewa kan gwiwoyinsa. cikin sanyi murya tace. "Nima marainiyace kiwo yakawoni kusadanan 6atan hanya yasakani shigowa nan hanyata nake nema amma nakasa ganewa. Cikin dubara yayi baya alamar tsoro ya buga kansa da bishiya sosai nan take yafadi Jini na fita goshinsa.   Hannu ta daga ahankali zata shafa ciwon danya warke ta dakata sbd karya sake tsorata idan ya farko.          Tashi tayi ta fara niman ganyayyaki tashiga haɗa mishi magani, tasaka mishi a ciwon,                Sun ɗauki kwanaki biyu a gurin tana kula dashi, tun ranar da duka haɗu sukayi magana bata ce mishi kome ba, tsakaninta dashi ido duk abinda majinyaci ke bukata take mishi. Zaman kuramen da suke ba karamin, haifar musu da wani shakuwa yayi ba, dan zata zauna a fakaice tana kallonshi, ko shi yayita kallonta, da zaran sun kama juna take kowanensu zai shiga kame kame, ba yanayin da suke yana tafiya da wani irin tsari na musaman, Jakarsa ta kaya ya bude ya buga tantin rumfarsa itace take kwana aciki shikuma yana kwanciya da wajen.        . . A hankali suke iya faɗawa junansu magana ko kuma hira sama sama, a wata safiya ya tashi ya zauna dake ciwon jikinshi ya warke yace mata. "Zan koma cikin gari, amma baki faɗa min sunanki ba, ni dai sunana Jamal ni maraya ne, zanje sake komawa gurin dangin iyayena dana gujewa.            Kura mishi ido tayi cikin nutsuwa tace, "Nima marainiya ce bani da kowa,sai kai da na haɗu da kai gashi zaka tafi kabarni Sunana Mineelik." Wani irin bugawa qirjinsa yayi sbd ambatar sunan kawai musamman duka kwanakin yayisu ne babu ko kyaftawar ido bare bacci sbd yasan rayuwarsa na tsakanin mutuwa da rayuwane idan yabari yayi kuskure dan qanqani taganosa.      Cikin tausayawa yace. Bakyason nabarki cikin dajin nan ne na zauna?          "Zanyi fatar haka idan ta kasance amma bazan maka dole ba." tace mishi.            Shiru sukayi, suka cigaba da satar kallon juna, a hankali shakuwar da sukewa juna ta sake samun matsaya na musaman ma inda ta rikiɗe ta koma soyayya mai matukar ɗaukar hankali,  tare suke farautar abinda zasu ci, idan zatayi wani abu zama yake ya kareta, gabaki ɗaya jamal ya sadaukar da lokacinsa sabida ita,, musaman suke zama suyita hira da zaran yaga ta fara alamun jin barci zai barta ta shiga ta kwanta yana gadinta. Tausayinsa ne mai tsanani yashiga rayuwarta sbd kaf baida abinda yake sai kulada ita tamkar sarauniya duk da baisan wacece itaba tabbas zata taimaki rayuwarsa kodan soyayyarsa data ginu a zuciyarta. #mamuhgee [7/30, 7:38 PM] ummul aulad: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *38* _a gaggauce_ _not edited_ Haske writers association. A gaggauce Not edited. Zaune suke dukkaninsu gaban boka aqoob dayayi shiru cikin jinjina mataki na qarshe dazai fada musu sbd aljanun dayake aiki dasu sune suke fada masa komai gameda sarauniya mineelik sbd suna cikin maqiyan farko na sarki penya. Kallonsu yayi 'daya bayan daya Dukkaninsu kowanne ashirye yakeda karbar matakin qarshe 'din sbd yanxu sunkai iya maqurar ganin cikar burin sbd Jamal dasukaga yafara shiga hanyarda bazata bulleuba su duka. Wasu irin qananan wuqaqe farare tas guda shida masu kamar azurfa ya fitar daga wani irin rami ya ajiye agabansu tareda kallonsu yace, Wannan wuqar dafin jinin penya ce wadda duk duniya ita kadaice zata kashe sarauniya mineelik, Kowannenku zai soketa da wannan wuqal agurare daban daban saidai kuma dafin zai illatatane bazai kashetaba matuqar ba masoyintane ya soketa da ita kuma ya zamto shine zaiyi mata suka ta qarshe da wannan wuqar to tabbas wannan ne kawai zai kasheta...idan Wanda takeso fiyeda komai bai soketaba to tabbas kusani sukarku zata illatane amma bazat mutuba Wanda kunsan rashin mutuwarta na nufin rayuwarmu mu duka dan haka wannan matakin na qarshe yafi kowanne hadari. Cikin zalama da qosawa kojo yace, Jamal bazai taba qi hakan ba koya gardama zamuyi amfani da qarfinmu mu sakasa. To bayan wannan kuma idan ta mutu to masautarta zata bace daga duniya babu Wanda zai sake ganinta saidai idan Wanda take tsananin so ya sadu da ita to tabbas idan ta mutu masarautarta tariga ta bayyana har abada tazama ta bil adama ta tashi daga duniyarsu. 'Daure fuska amari yayi zaiyi magana da sauri kojo ya dakatar dashi yana cewa, Munriga munkawo yanzu babu abinda zai gagara yamaida mu baya ga wannan tafiyar Jamal dole zai sadu da sarauniya mineelik. Wasu sabbin madaurin damtse na wani tsarin boka yabasu kowannensu ya daura tareda 'daukar wuqa 'daya na Jamal kuwa cikin fata amari ya nade masa ya soka qugunsa suka miqe. Yonas dake qoqarin soka tasa cikin takalmin fatar damisarsa yaji hannunsa na wani irin qaiqayi yayi saurin dubawa zai sosa saiyaga rubutu na bayyan a hannun nasa yayi saurin kallon mahaifinsa yaga idanuwansa rufe alamar saqone yake ruboto masa dan sanar dashi wani abin. Da sauri ya maida kallonsa ga tafin hannunsa yafara karanta saqon. "" idan buri ya kammala kawai da datti ake ashare komai da komai"""" Jinjina kai yayi cikin rashin tausayi yakalli bayansu kojo dasuka gabansa dan yafahimci saqon meyake nufi yana nufin idan ankammala su kashesu nan take. Suna fitowa qofar gidan boka aqoob sukaga wani irin gini mai matuqar tsawo da kyawu tareda girman dabasu taba ganiba mutanen gari sai fitowa kallo akeyi ana nufar hanyar da ake hango masarautar Atake cikin gaggawa suka hau raqumansu suka nufi hanya sai tun daga nesa suke hango babu daji sai masarautar kawai da girmanta yasa ta zamto kamar tana cikin ganin ne. Suna isa bakin qatuwar qofa mai girman gaske suka taru su biyar suka tura qofar tabude suka shige cikin wani irin mamaki mai rikita tunani da nustuwa sbd girma da kyawun masarautar babu kowa koina tsit saidai komai fes tamkar yaune aka ginata. Harabar gurin suketa rarraba idanu suna kallo cikeda far in ciki mara misaltuwa sbd burinsu yacika saura qiris su mallaki sauran duniyar. Wasu furanni masu qamshi yonas ya tsinka ya shinshina ya lumshe ido cikin farin ciki ya daka wani tsalle tareda sakin ihun farin ciki. Kojo kuwa mahaukaciyar qofar daya tabbatar ta fadar da karagar ke cikine ya nufa ya saka hannu biyu yatura qofar ta wangale atake dukkaninsu sukai mutuwar tsaye ganin karagar dake wani irin daukar ido duk da kasancewarta kalar baqa mai adon zan zinari. Girman fadar suka kallon cikin wani irin farin ciki madaukaki da sauri suka nufi kujerar kusan atare kowanne na burin kaiwa ya hau Jamal yasha gabansu cikin wani irin yanayi na damuwa da bacin rai. Tsayawa sukayi dukkaninsu kallonsa saidai ganin kamar hawaye cikin idanuwansa yasasu tamvayarsa cikin gaggawa. Yaja baya tareda zubewa kan gwiwoyinsa murya na rawa yace, Ina roqonku da karku cutatar da ita domin kwadayin arzikinta kubari zankarbar mana ta hanya mafi lalama da yardar ta. Wucesa amari yayi ya nufi karagar yana banzatarda zancensa sbd har abada babu Wanda zai shiga tsakaninsa da wannan taskar arzikin. Dukkaninsu babu Wanda yabi takansa sbd babu alamar gudu ko ja da baya a wannan alamarin nasu. Cikin wani irin gunjin kuka ya durqusa a gurin suka waiwayo suka kallesa ajani ne yadawo gabansa ya tsaya cikin kulawa yace, Meke faruwa munyi alqawarin duba damuwarka idan kafada. Kallonsu yayi cikin wani irin gunjin kuka mai ciwo ya girgiza kai yana cewa, Ayau na hada shimfida da sarauniyar aljanu Wanda na tabbarda hakan wata sabuwar qaddara rayuwa ke nufi dani saidai kuma hakan y juyar da ra'ayina bazan iya cutatar da itaba sbd a duniyarsu hakan wani babban alamari mai tsananin girma yake nufi dan haka ta tafi wani gurin bauta bazata dawoba sai bayan kwana uku sbd abinda yashiga tsakanina da ita zatajene domin dawowa duniyata gaba daya dan haka nake roqonku karkuyi abinda zai barmu da masifar da bazata tsaya akanmuba kawai. Cikin tsananin farin ciki da jin dadi suke kallonsa atake dukkaninsu suka sheqe da dariya mai qarfi cikeda farin cikin ganin komai ya tabbata qiris yarage. Kallonsu yake daya bayan daya yana mamakin dariyarsu cikeda fargaba. Sake kutsawa cikin masarautar mai girma sosai sukayi kowanne na taba abinda ya burgesa duk wata zalamarsu da kwadayinsu ya fito nan suka ringa shiga dakuna da gurin shaqawata da sassa daban daban babu tsoron komai aransu. Shikuwa ke6e kansa yayi daga garesu yana zullumi da tunanin manufarsu daya kasa ganowa yadai San dole sunada qudirin cutatar da ita. Ranar data cika kwana uku a makeken lafiyyan dakinta dake turakarta ta bayyana lokacin yana zaune tsakiyar daki cikin tsananin tashin hankali da damuwa. Kallonsa take cikin tsananin farin ciki da wani irin yanayin jin dadi takira sunansa cikin qauna da soyayyarsa. Da sauri ya miqe tareda juyowa bata tsaya bata lokaciba ta rungumesa da qarfi tana sake ajiyar zuciya cikin farin cikin kasancewa dashi har mutuwarsu. Rintse ido yayi sbd tuno abinda yafaru ayau tsakaninsa da 'yan uwansa. Wuqar da boka yabasu suka fitar masa da yasa suka basa tareda yimasa bayani yayi saurin wurgi da wuqar yace, Aikuwa idan har nine Wanda kawai zai iya kasheta har abada bazata mutuba. Cikin takaici kojo ya kallesa yace, Baka isa ka rusa mana shirinda muka share shekara da watanni muna sadaukar da rayuwarmuba. Kabarsa yagama bulayin shirmen son wadda ba jinsinsa idan yagama shirmrn mafarkin zaidawo hayyacinsane lokacinda tagano manufarsa ta aikasa gurinsu dede"""cewar amari dayafi hasala da zancen. Yonas ya sake dauko masa wuqarsa ya saka masa cikin hannunsa yace, Idan bakayiba mu zamuyita sukarta harsai ta mutu koda zamu dauki shekara dari ne saidai kasani tana warkewa karasa yan uwanka dasune rayuwarka har abada sbd kashemu duka zatayi kuma harda kai aciki. Ajani dayafi kowa qaguwa dasu mallaki masarautar ya matso gabansa ya tsaya cikin tabbarwa yace, Zabi yarage naka kazaba 'yan uwanka ko soyayyarda bazata doreba har abada sbd ba jinsi dayaba dan haka kashirya tana dawowa zamu qarashe aikinmu idan baka yi yanda akaceba kana kallo zata kashemu. Tafiya sukayi sukabarsa tsaye da wuqar ahannu yana kallo cikeda wasi wasi saidai bazai iya bari yarasa yan uwansaba sbd sune rayuwarsa sunayiwa juna wani irin so da qauna mai qarfi. Zamewa yayi daga jikinta jin kamar wani abu a gabanta kallo daya yayi mata yayi baya da qarfi  cikin wani masifaffen tashin hankali sbd ganin qaramin ciki ajikinta. Matsosa tayi cikin farin ciki tana Murmushi zatai masa magana yasake ja baya tareda ficewa da sauri. Dayake safiya ce sosai sauran babu Wanda yatashi suna sassansu kowanne yazabi sashensa sunacan suna hutawa tuni suka samo masu hidima. A cikin fadar ya shiga ya tsaya jikinsa na wani irin rawa zufa na karyo masa takoina Ta bayyana a gabansa tareda riqo hannunsa ta 'dora akan cikin ahankali tace, Cikine dani kuma........cak ta tsaya da maganarta jin sukar data sauka ajikinta daga bayanta Cikin wani irin yanayin azaba ta juyo dan ganin waye taji wata sukar a gefen cikin duka biyun. Jajayen idanuwanta ta 'dago cikin radadi da azaba takallesu amari ne da yonas, Jinine ya fara fitowa daga hancinta ta 'damqe hannun Jamal da idanuwansa suke zubarda wata irin qwalla da kuka mara sauti, kojo da ajani tareda haji suka tsaya gabanta tareda 'daga wuqaqensu suka soketa da qarfi aciki lokaci 'daya. Tasake damqe hannun Jamal tareda fitarda wani nishi mai qarfi da wata irin azaba atake Jini ya balle mata mai matuqar yawanda basu taba ganin irinsaba hakama bakinta yafara fitarda jini ta yanke jiki ta zube bakin karagar mineelik tareda kallon Jamal daya fiddo wuqarsa yana hawaye ta lumshe ido cikin tsananin baqin ciki mai tsananin gaske sbd ta tabbatarda cin amanarta da yaudararta sukayi ahankali tabude baki daqyar ta furta, Duk iya alqawari da soyayyar danake maka meyasa kazabi cuatatar dani., Karka kasheni kabarni na rayu kodan cikinka dake jikina nikuma zan maka alqawarin sabuwar rayuwa, Haryanzu zuciyata nasonka ko ka kasheni bazan daina sonkaba....... A hankali ya 'daga wuqar ya nufi qirjinta yana kuka yashigarda wuqar qirjinta da qarfi. Atake tasaki wani irin azababen nishi mai qarfi daya amsa masarautar gabaki daya ta kallesa idanuwanta na fitarda wasu irin hawayen ahankali ta bude baki tace, Meyasa???? Cikin izza ajani yace, Sbd karagar mineelik. Kallon Jamal tayi ya juya mata baya yana sake sakin sabon kuka ta kalli karagar tasaka hannu ta debi jininta dake zuba ta zubawa karagar ta lumshe ido sbd wata irin azaba dake ratsata cikin, Hawayen azaba tace, Ayau ni sarauniya mineelik 'yarda,soyayya dakuma amincewa yasa bawa mafi soyuwa a rayuwata ya kasheni ya zubar da jinin 'dana ko 'yata dan haka haqqin jinana bazai taba barin bibiyarku ba har qarnin qarshe harsai ranarda jini ya maida jini maimakon jini dan haka nayiwa mineelik baki zata zame muku masifa mara magani da ganewa,,,,daga yanxu jini ya ringa zuba kenan amaimakon jinin 'dana. Kallon bayan Jamal tayi lokacinda taji ko maganar takasa sbd tsananin azaba ahankali ta furta nabar maka dukiyata sbd sarauniya bata alqawari ta 'daga saidai bazakaji dadinta ba...... Cikin rashin imani yonas ya daga wuqar ya soke mata maqogoro atake ta saki numfashi da ajiyar zuciya ahankali jikinta ya saki ta bace 6at. Zubewa agurin Jamal yayi yana wani irin kuka mai sauti. Cikin tsananin farin ciki da murna amari ya nufi karagar zai hau boka aqoob ya bayyana gabansa cikin wani irin murmushin mugunta yace, Nine mai hawa wannan karagar duk Wanda ya........bai qarasaba sukaga kansa ya fille yafadi qasa. Kojo sukaga yani a bayansa kenan shine ya fille masa kai Cikin murna ajani ya nufi kojo zaiyi magana yonas ya sha gabansa cikin tsananin baqin ciki da zafin zuciyar ubansu da aka kashe yana 'daga wuqarsa zai cirewa ajani kai aka soke masa zuciya daga bayansa saida takobin ta fito ta qirjinsa. Wanda amari ne yayi wannan aikin. Haji na ganin haka ya juya da gudu ya fice yace, Kusani wannan gabace da masifar dazata zo har zuriar zuriar bayanmu. Cikin zaquwa amari ya juya zai hau karaga Jamal ya buge qafafunsa tareda miqewa ya isa karagar kai tsaye ya hau ya zauna tareda kallonsu da jajayen ido yace, Nine magajin mineelik dan haka nine zanyi sarautar duk Wanda hakan baimasaba yana buqatar hada kwanji dani. Kallon juna sukayi ga mamakinsa saiyaga sun nuna amincewarsu. A ranar Jamal ya karbi sarautar mineelik kuma aranar aka dauki masu hidima 'Dari da hamsin atake masarauta ta cike da mutan gari ko sati ba'a rufa dukkaninsu sukayi auren mataye uku uku lokaci 'daya, Mineelik cikin qanqanin lokaci tazama masarauta mafi girma da iko a wannan qarnin musamman data zama babban gari mafi girma Kafin mulkin Jamal yaqare saida mineelik takoma itace a tsakiyar babban birnin Ethiopia sbd cika da garuwan qasar sukayi koina ya cike tazama babbar qasar cin kasuwar jiragen ruwan dake wajen gari. Mulkin Jamal wani irin mulkine na daukar rayuka ba abakin komaiba, Suna arziki da yawa da girma babu kamar mineelik a wannan qarnin sbd garin da masarautar take ko zakayi wata daya kana yawo bazaka zagayesaba. Duk wani burinsu Jamal dasu kojo yacika saidai rashin haihuwar 'yaya maza daya addabesu daga qarshe har sultan jamal ya rasu bai samu 'da namijiba sai mata Bayan saukarsa sultan kojo ya hau shima duk tsawon shekarunsa harya mutu bai haifi namiji ba dukkaninsu sunyi mulki ajani kawai yasamu namiji 'daya acikin 'yayansa Wanda bayan rasuwarsa shima dansa sultan amed yahau bayan sultan amed sai sultan nurin,dagashi sai sultan abaass da haka mulkin yayita zuwa qarni qarni so 'daya akayi assultana Wanda mulkinta karagar tafi ta6ata kasanewarta mace, Alokacin mulkin assultana ankashe rayukane tamkar dabbobi sbd jini daya yawaita a mulkinta sbd iya zubar jini iya qarawa karagar qarfi qarshe abin taba kwaqwalwarta yayi ta samu tabin hankali ahaka ta rasu. Da haka 'daruruwan shekaru suka shide musuluncin gske yashigo cikin qasar suka karbesa sosai inda a yanxu suna cikin qasashen dasukafi yawan musulmai duk da wasu haryanxu suna aladar bin bokaye. A yanxu muna wani lokacine na waye da ilimin zamani tareda qarni mai dadi sbd rayuwar ilimin boko dana addini daya shiga koina ya wadata. Sultan abdulshams sarkine mai tsananin son kansa fiyeda duk wani abu a duniya har yayansa har matansa shidai arayuwa kansa yasani shiyasa yadau alqawarin karya alkadarin mineelik domin yaci gaba da mulkinta shikadai sbd shikansa yaxubarda jinin alumma fiyeda qima dan haka yanason mulkin bazai barshiba shiyasa yayi bibiyar yanda zaiyi yagano ma'anar kalmar, """"jini ne zai wanke jini domin jini"""" a cikin littafin tarihin masarautar mineelik. Ma'ana soyayyace tamkar wadda takewa jamal mai hadeda jinin cikinta zata karya wannan masifar shiyasa azamansa da bawansa bulama ya fahimci wata irin qauna da soyayyarsa da matarsa yayi amfani da qarfin ikonsa yasa jakadiya ta ware musu wata 'daya suna kebantuwa da juna ranarda Jakadiya tagano asma'u ta samu wani cikin tasanarda sultan nan yafadawa sultana zaarah nufinsa bawai danta hanaba saidanta kawo masa asma'u gaban karagar da safe daidai irin lokacinda aka kashe sarauniya mineelik. Badan sultana tasoba saidan tsananin iko da barazanar sultan agareta ranar wata laraba da safe tashirya tace Jakadiya tasa asma'u cikin 'yan rakata gurin sultan kai gaisuwa. Koda suka isa tace asma'u tabita suna shiga suka rararda bulama tsaye yana jiran fitowar sultan nan sultana tashiga gurinsa tabarsu tsaye suka qurawa juna ido cikin qauna da soyayyar junansu ya kalleta cikin nutsuwa yace, Idan kika haihu ko bananan kisawa yaron suna bilal idan mace ce kisaka mata asma'u. Murmushi tayi zatai magana sultan da sultana suka fito sultan yakallesu kafin yayi magana Jakadiya tashigo daukeda qaton tray daukeda kofuna guda biyar takai gaban sultana da sultan suka dauka ta juyo ta miqawa bulama 'daya asma'u 'daya babu musu suka karba sultan yace, Wannan taya murnace ga bawana bulama na 'yantasa daga yau. Cikin tsananin farin ciki suka zube qasa suna godia sbd sunsan nesa tazo kusa sunkusa komawa qasarsu kenan. Cikin tausayi Jakadiya tace, Kusha kyautar sultan Ku godewa Allah. Da sauri suka kwankwade lemon suna sake godiya suka miqe suka fice sultana ta sauke numfashin damuwa da tausayinsu tareda baqin ciki da dana sani Wanda take kallon kanta amatsayin wadda takashesu shiyasa take tsananin qaunar yarsu. Acikin daren bulama ya rasu da ciwon ciki asma'u ma ta rasu da cikinta dabata haifeba Wanda babu Wanda yasan dashi saisu dasukai aikin saidai abinda basu saniba shine kozaku sadaukar da rayukan masoya 'Dari to masifar mineelik bazata karyeba sai masoyan dasuka kasance sunada jini da masarautar. ** A matuqar gigice ta farka a firgice suka miqe tsaye amatuqar firgice suna watsa ruwan magani sbd basusan a yaya ta farko ba. Maheer dake zaune hannunsa cikin na suhailat ya zare ya miqe ya nufi gadon yana kallon fuskarta dake bawa duniyarsa nutsuwa. #mamuhgee. [7/30, 7:38 PM] ummul aulad: _*TARAYYA*_ _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *37* _Not edited_ _a gaggauce_ Haske writers association Shiru tayi tana kallonshi cikin nutsuwa, ta rasa ta inda zata fara  taimakonshi satar kallonta yayi cikin nutsuwa, sannan ya sauke numfashi yace.            Rayuwarsu a dajin wani irin rayuwa ce, mai ɗauke da soyayya da wani irin kulawa ba daga itaba har zuwa ita kanta. Mafi lokuta takan zauna tayita tunani anya ba wani kuskure bane yake shirin afkuwa na amincewa bil'adam, sai wani ɓangare na zuciyarta ya tuno mata tarin alkhairin da Jamal yake mata,               Wani lokaci suna zaune ta kalleshi, a nutse kafin tace, "Menene silar barowarka daga gida ka shigo wannan dajin har kake tunanin kashe kanka da rayuwarka."                Kirjinshine ya bada wani irin sauti, kura mata ido yayi yana qoqarin qin barinta gano yanayin daya shiga cikin daidaita  nutsuwa sai ya sunkuyar da kanshi cikin nuna baqin ciki yace, Idan kika san abinda ya baroni da dangina sai kema kin gujeni, labarina ba labari bane sbd cike yake da bakin ciki.   Dafe goshinshi yayi yana dauke kai yana girgizawa cikin damuwa mai tsanani sannan ya cigaba da cewa, "Idan kika san koni waye guduna zakiyi gwara mubar maganar haka dan babu alkhairi a ciki.          Wani irin qayataccen murmushi tasaki cikin qasaitar mulkinta dabatamasan tayiba tace, Kayi min halacci zama tareda ni kana kula dani tamkar nauyina yana rataye akanka dan haka bazan gujekaba fadamin.            Girgiza kai ya cigaba dayi yana cewa, Karki so jin waye ni, karki so jin waye ni, labarina cike yake da kayan haushi da bakin ciki.            "Ko baka  yarda dani bane, dan idan ka yarda dani ai babu abin bakin ciki a jin kai waye saima karin amintaka a cikin zamanmu.   Gyara zama yayi zuciyarsa cike fal da farin ciki dan abinda zai fada mata shine matakin nasararsu.       "Kamar yanda na faɗa miki ni marayane bani da uwa bani da uba, amma akwai kawunaina, kasancewar iyayena sun mutu basu bar min ko 'dayaba koda kuwa kaza ce yasa na zama abin tsangwama a cikin mutane, sannu a hankali na fara niman nawa na kaina sai dai...            Kura mata ido yayi cike da jin ba daɗi da kuma hango yarda da Amana da tabashi sai ji yayi akaron farko bazai iya cika wani mugun kudiri a kanta ba, sunkuyar da kanshi yayi cikin wani irin yanayi na sanyin jiki wanda bawai dan maganar da yake mata bane sai dan akaro na farko da zuciyarsa ta hango masa  kuskure da suke shirin tafkawa ne Wanda zai iya bibiyarsu har jikokin jikokinsu na qarni mai zuwa.          Cikin nutsuwa tasake kiran sunansa tace, Karka damu nimai riqe sirrinkace.    "A'a mineelik ina tsoron karki guje nine.                 "Ina tare da kai nace ka yarda dani.     Gyaɗa kanshi yayi sannan yace, "Nayi kokarin neman nakaina amma abu yaci tura daga nan kome na taɓa sai ya lalace kai ko kayan mutane na taɓa ya tashi aiki sbd baqin Jini da baqin qashin tsiya da'ake cewa inadashi daga nan mutane suka shiga jifana da mai kashin tsiya bani da albarka a rayuwa haka bai isheni ba sai na faɗa niman aure nanma mutane suka shiga korata a kofar gidajensu suna goranta min ynx waye zai yarda ya bani auren ɗiyar shi yanda tsiya da fatara ya kewaye rayuwata, Qarshe ko qofar gidajen mutane sunhanani bi idan nabi qofar gidan mutum aranar saiya rafka babbar hasara tou tsangwama da qyama yasa nabar garin nashigo duniya shi yasa na shigo dajin nan sbd jin labarin ha'darinsa naso koma meyene aciki ya kasheni.      Abin tausayi abin dariya yar karamar dariya tayi wanda ya bayyanar da jerun kyawawan hakoranta farare.                    Ganin irin kallon da yake mata yasa ta ɗan rufe bakinta cike da qaunarsa mai qarfi dake zuciyarta tace, "Tabbas akwai abin dariya a rayuwar bil adama sbd kamar munfisu yarda da qaddarowar Allah ne. Kallonta yayi da sauri cikin rawar murya yace, Mekike nufi da bil adam ke kincire kankine daga bil adaman? Kallonsa tayi cikin takaicin zancen datayi ta girgiza kai cikin son gyara zancen tace, Dukanmu bil adama ne saidai wasunmu kamar basuda daukar qaddara sbd banga abin gudu da qyama ananba.        "Hmm kece kike ganin haka amma abin ba haka bane, aiku mata baku ɗauki kome da muhimmanci ba, tunda ba damunku abin yayi ba. Girgiza kai tayi ni na amince zan aureka a duk yanda kake sile 'daya sun wadaci sadakin auren.      Mikewa yayi a razane tare da tsorata sbd baitaba kawo wata maganar aure atsakaniba yace, Banda komai dazan inganta rayuwarki na kare martabarki amtsayin mijinki dan haka bazan iya lalata miki rayuwa ba.              Jikintane yayi matukar sanyi har tana dana sanin fada masa hakan sbd har cikin ranta takejin damuwarsa sbd tausayinsa mai qarfi da yayi wasi zuciyarta kamu tareda soyayyarsa mai qarfin gaske dan haka zata inganta masa rayuwa, Zata basa kaf arzikinta saidai zata daukesa sunkoma duniyarta rayuwa acan zaifi musu dadi.               Ahankali ya furta idan har kin amince da aurena a yanda nake dinnan tabbas zan sadaukar da rayuwata gurin nema dan inganta miki rayuwa.    Yarda dashi yasa take kwanciya tayi baccinta batareda sakin dukkanin jintaba shikuma yana ganin tayi nisa a bacci            yasaci jiki ya nausa yamma da saurinsa da gudunsa sai tsakiyar dare sosai ya isa inda su Ajani suke tun daga nesa yake musu kukan wata tsuntsuwa dansu gane shine tafe dan karsu harbo masa hari daga nesan. suna jiyosa cikin bacci duk suka  mike Suka fito rumfarsu yana isowa gabansu ya zube a wahalce yana fitarda numfashi tareda sakin ajiyar zuciya.        Amarine ya rungume shi cike da kewar kanin nashi yace, "Da fatan anyi nasara?                 Murmushi yayi ya nemi guri ya zauna, sannan yace, Nasara tazo ne tareda matsala sbd tace na aureta.    Nan ya faɗa musu komai.                  Shiru sukayi kafin Haji yace,     Toh ba zaiyu bane mu karɓi dukiyar da karfin cin tuwo basaika auretaba. Wani mugun kallo amari yasakar masa zaiyi magana yonas dan boka yace, Meya hana kai kaje gurinta sauka karbo da qarfin cin zaki bama na tuwo ba. Zaburowa haji yayi tareda fisgo takobinsa mai tsananin kaifi ya nufi wuyan yonas Jamal yayi saurin tarewa yace, Ba yanzu zakuyi wannan ba kubari mukarba daga baya kun kashe kanku,kafin ya kalli haji din cikin ido da Wani irin kallon banza dayayi masa cikin rashin jin daɗi abinda yace,       Lallai kusani koda barazana bazan karɓi dukiyarta ba sai da amincewarta.    Arazane suka hau kallon juna cikin wani irin mamaki da tabbarwa da maganar da boka yafada musu bayan tafiyar Jamal din da dayansu yaje. ganin irin kallon da sukewa juna yasa shi shan jinin jikinshi sbd kuwa ya tabbatarda akwai wani abu dasuke boyewa. Kuna qoqarin boye min wani abune akan mineelik?     Babu Wanda ya basa amsa sai kojo dayace masa, Ko 'daya kashirya gobe zamuzo amatsayin nemanka muke daga nan zamu daura auren muyi abinda yakawo mu muje wata harkar sbd idan muka tsaya sanya zamu qarasa rayuwarmu ne a wannan dajin.      Juyawa yayi zuciyarshi bata aminta dasu ba ya fice yana tunane tunanen abinda suke boye masa dan kuwa yasan tabbas akwai abinda suke boyewa.           Bayan tafiyarshi Kojo ya kalli  Ajani cikin bushewar zuciya da takaici yace,    Aqoob yayi gaskiya na cewar Jamal zai iya fara sonta na hango damuwa a cikin idanunshi ba jarumta ba kuma da zaran yasan da kudirinmu akan mataqin qarshe na mallakar dukiyar toh ba zai taɓa yarda damu ba kuma komai zai lalace.       Shiru sukayi dukkansu sbd bazasu taba bari banzar soyayyarsu ta kaisu ga rasa abinda suka sadaukar da rayuwarsu gurin nemaba. Koda ya isa asuba tayi har haske ya'dan fara yayi saurin kwantawa yana wasi wasi akan mineelik da abinda suke boye masa, hango wautarshi yayi da ya amince da bukatar ya yaudareta sbd yadaura ko a tsakaninsa da bil adama yar uwarsa ne haqqi baya barinka bare sarauniyar aljanu mafi hadari ko acikin sarakunan. yana gurin har gari ya waye kafin tafito ya shiga daji nima musu abinda zasu ci.           Koda ya dawo taga rashin walwala akan fuskarshi tambayarshi tayi ko akwai wani matsala yace, Babu kai tsaye yana juya mata baya sbd bayason kallon fuskarta yanzu jin yake zuciyarsa na karyewa da abinda suke shirin yi yanajin kamar bazai iyaba.          Shiru tayi ta cigaba da zama tana satar kallonshi da zaran sun haɗa idanu zata ɗauke kai tana murmushi haka shima yake qaqalo murmushin qarfin halin.            Kusan ita tayita janshi da hira, har ya sake da ita suka cigaba da hidimarsu can suna zaune sai suka jiyo sautin muryan mutane na doso inda suke mikewa tayi ta koma bayanshi tana leka inda take jin muryan mutanen. Shikuwa dayasan da zuwansu bai wani nuna damuwaba saidai fargaba da wasi wasin abinda sukazo ayi wato auren. Tabbas yanajin wani irin tsoro, fargaba shakku da wasi wasin aikatawa. Cikin nutsuwa suka tunada gargadin boka aqoob dayace saisunyi matuqar taka tsantsan karta zargi wani abu ko taganosu dan kuwa rayukansu zasu rasa dukkansu idan aka samu matsala shiyasa        Su ajani ne suka iso har inda suke ja yayi da baya a tsorace su kuwa suka diro raqumansu da wani irin tsuma da far in ciki jikin na rawa suka qaraso gabansa cikin babbar murya kojo yace, Jamal kasan abinda kayi da halinda kasamu ciki daka gudu aka rasaka? Fiyeda kwana hudu muna yawo cikin dajin nan nemanka bayan mun share satittika muna yawon qauyuka nemanka mekakeyi wannan hadararen dajin....?     Kuka ajani ya saka cike da bakin ciki yace, "Yau da ɗan uwanmu na raye ai kafi karfin wulakacin badan haji yace mu shigo ta daji ko kazo ka rataye kanka ba, Gidanmu ya qone qurmus bayan barowarka shiyasa muka tabbatarda zamanka a gidanma kuma wata rahamace kayi hakuri mu koma musan yanda zamu dora itace muyi wani gidan bazamu sake bari a wulaqantakaba zamu samo maka mata mu daura maka auren dakakeso.           "Babu inda zani dan ni na sami wacce zata aureni da zuciya ɗaya bata damu da dukiya ko arziki ba. Cikin Sauri da 'doki yonas yace, Zamu aura maka ita yanzu dai kazo muje gida idan munje a daura maka ita acan tunda yanzu idan anyi bakada gurin sakata.              Shiru yayi alamar nazarin zancen kamar gaske. Ita kuma cikin nutsuwa takallesa ganin yashiga tunani ta dafashi ahankali ya matsa mineelik ta bayyana daga bayanshi.       A tsorace sukayi baya zuciyoyinsu na rawa saidai jaruman gaske ne bazasu bari kyawunta da kwarjininta ya rikitasu ba.       Cikin sauri kojo yace wannan ba irin matarka bace bazata zauna dakaiba idan taga talauci zai illatata.      "Na rantse da abin bauta bazan barta ba ina sonta kuma zan aureta idan kuka ce bazaku barin na aureta ba zan kashe kaina na huta.    Cikin fusata Amari yace. "Ka daɗe baka mutu ba wannan matar tafi karfinka ka nemi wata mana kokuma mu munema maka wata.       Ahankali ta matso kwarjininta da wata irin haiba dake fitowa daga gareta na girgiza zukatansu saidai buri da kwadayinsu yasa suke kannewa cikin jarumtarsu cikin wata irin murya mai dadi tace, Ku auramin shi nikuma na muku alqawarin taskar arzikinda dar qarnin qarshe zuriarku bazatai talauciba, Ina sonsa zan auresa ahaka kuma nayi alqawarin ko bayan mutuwa zan qaunace bazan barsaba wannan alqawarine daga sarauniya datafi kowace sarauniya mulki, wannan son dayake min yafi min kome a duniya.      Wani irin kallo sukayiwa junansu cikin gamsuwa da burinsu yazo a sauqin dabasu taba tsammaniba. Kojo ne ya matso gabanta suna fuskantar juna cikin rashin tsoro yace,       Mun amince zamu daura muku aure a yanxu basai anje koina ba saidai bawai dan kinada arzikin dazaki bamuba dan da alama kema nema kikeyi.      Murmushi tasaki ahankali tareda kallonsa takalli sauran dakuma raqumansu tace. Idan sarauniya tayi alqawari bata canxawa, Alqawarinta kamar rubutu ne akan dutse har abada baya canxawa.         Murmushi yonas yayi tareda kallonta cikin ido yace, Mukuma alqawarinmu idan muka dauki burin abu kamar rubutu ne ajikin dutse baya goguwa sai muncimmasa. Murmushi tayi tace, Buri da alqawari basa haduwa sbd 'daya saiya danne 'daya yake tabbatuwa amma Ku sani zaku tuna hakan wata rana. Kallonta sukayi a 'dage kafin amari ya kalli Jamal daya qura musu ido cikeda tunani kala kala aransa game dasu yace, Yanxu za'a daura aurenka da sarauniyar ranka saidai kasani soyayya gubace mai kaifin gaske kafadawa 'yaya da jikokinka wannan. Shigewa tayi tantinsu tana jin wani irin yanayi na farin cikinda bata taba jinsaba sbd tana yiwa Jamal wata irin soyayya da qauna mai qarfi dazata iya sadaukar da komai kansa ciki harda rayuwarta. Atake suka rabu biyu suka wakilci ango da amarya aka daura auren da sadakin sile 'daya. Bayan daura auren ne sukace zasu tafi su dawo sbd boka aqoob dayace idan andaura suzo yabasu matakin qarshe. Bayan tafiyarsu da daddare yana zaune ya kafawa wutar daya kunna ido shikadai gabaki daya zuciyarsa cikin wata irin dana sani da qunci take sbd abinda yakeji gameda mineelik bazai iya cutatar da itaba saidai kuma bazai iya fada mata komaiba ko yayi gangancin bari tagane sbd rayuwar 'yan uwansa dan yasan shi tana masa so mai tsananinda bazata iya kashesaba ko illatasa. Ahankali yakejin sautin qarar sarqar qafa da taku na nufosa tareda wani irin haske da niimtaccen qamshin mai tareda sanyi na shigarsa ya 'dago ahankali ya qurawa gurin ido baiga fuskartaba sbd wani irin kyallin zinari dake fita daga wuyanta da kanta tareda damtsen hannunwanta da qafafunta sbd adon sarqunan dake jikinta. Saidatazo gaf dashi ta tsaya cikin ainihin suffarta tana sakar masa wani irin murmushi mai qayatarwa ta miqa masa hannunta cikin wata irin murya mai dadi tace, Ina tayaka murnar zama attajirinda babu kamarsa a wannan qarnin, Ina taya murnar zamtowa mijin sarauniyar da babu tamkarta a wannan qarnin, Soyayyace farko kuma soyayyace qarshe, Zan rayu dakai na bauta maka domin Kaine sarki a masarautata saidai cin amana,qarya da yaudara basa cikin soyayyata basa cikin abinda nake dubawa amatsayin kuskure koda ga abinda nafi so ne. Murmushin takaicin rayuwarsa yasaki sbd yasan tunda ya bari zuciyarsa takamu da soyayyarta rayuwarsa na tsaka sbd bazai iya rabuwa da 'yayan uwansa ya 6ata musu buriba sannan bazai iya bari acutatar da itaba. Cikin sanyin murya data nuna zallar damuwar dayake ciki yace, Wacece ke? Ahankali ta furta, Sarauniya mineelik,aljanarda aljanu da mutane suka buri da fatar gani kuma matarka ta har mutuwa. Rintse ido yayi akaro na farko yaji jarimtarsa ta 6ace ya sauke kai cikin rawar murya yace, Meyasa kike sona har haka bayan bakida cikakken sani akan abinda yake zuciyata. Ahankali ta 'daga hannuwanta sama tayi budesu idanuwanta akansa tace, Barka da zuwa masarautar mineelik. Miqewa yayi cikin wani irin mugun tsoro da firgici yake kallon koina yana jujuyawa kamar wuyansa zai cire sbd ganinsa Cikin wata irin masarauta mafi girma da kyawun dabai taba ganiba duk yawon duniyarsu. Adon ne zaibar zinari da wani irin gini mafi kyau da tsari Wasu irin kujeru ne a Jere na sarauta sunsha ado wani irin ni'imtaccen kamshi na tashi daga  yanayin jerin kujerun da tsarinsu yasa ya tabbatarda nan ne asalin fadar wato dakin taron sarauta. Wani irin qyalli yaringa gani yana hasko bayansa yayi saurin Juyawa a kidime yaja da baya tareda zubewa qasa kan qafafunsa yana kallonta cikin wani irin tsoro da firgici.. Zaune take kan karagar mineelik tafito masa Zak amatsayin sarauniyarta atake wani irin tsoronta da firgicin dabai taba jiba yasashi sauke kai yana girgizawa. Ta bayansa yaji andafasa a zabure ya juya yaga itace yayi saurin kallon karagar yaga bata kai ya juyo yasake kallonta ta sakar masa murmushi mai sanyi tace, Banason sanin sirrin dake zuciyarka sbd idanuwanka sun tabbarmin da abinda nake nema daga gareka wato soyayya mai qarfi dan haka masarautar mineelik takace kaima daga yau dakazama mijin mineelik. Murmushin baqin ciki yasaki tareda miqewa ya juya mata baya cikin tsananin damuwa yace, Idan 'yan uwana sunzo basu ganmuba zasu....... Masarautar mineelik ta bayyanane ga dukkanin Wanda ke wannan nahiyar sbd duk girman wannan dajin da mutum zaiyi tafiyar kwana bakwai bai gama fitaba acikinsaba ba daji bane duk girman masarautar mineelik ne dan haka ayanxu mutane na kusa da nesa suna hanyar zuwa kallon masarautar dabasu taba gani ba ta mineelik data bayyana ga kowa. Zai sake magana taga duk cikin tashin hankali yake mai tsanani Ahankali ta riqo hannunsa cikin nata tsananin laushi da ni'imar fatarta yasashi kasa magana yabita tamkar raqumi suka nufi turakarta datafi kowace kyawu. #mamuhgee [8/1, 7:44 PM] ummul aulad: _*TARAYYA*_ _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *39* _not edited_ Kallonta yayi da idanuwansa dasukai laushi sbd damuwa Ahankali ya qarasa bakin gadon Negasi ya bude baki zai dakatarda dashi ya daga masa hannu ahankali cikin mulki da bada umarni ya bude baki yace, Ina buqatar ganawa da ita. Cikin girmamawa suka fara ficewa ammy dake kallon rumanah kamar idanuwanta zasu fado zuciyarta na bugawa da sauri gabaki daya bata cikin nutsuwa so take taji rumanah tayi magana tasan halinda take ciki saidai rumanar idanuwanta a rintse suke Kowa ya fice sai ammy da suhailat dake bayanta tsaye rungume da abeel zuciyarta na rauni. Ahankali ya zauna kusada ita bakin gadon ya riqo hannunta ya damqe cikin nasa tareda qurawa fuskarta ido Ahankali ta bude idanuwanta dasukai jajir ta kallesa zuciyarta na harbawa da sauri, Zuciyarta qoqarin kallonsa takeyi a matsayin a iyayensa sukayiwa nata iyayen kisar ganganci da rashin imanin abinda ke cikin mahaifiyarta saidai kuma Sam zuciyarta takasa jin sauyi ko tsanarsa dan kuwa itama tana masa wani irin so ne Wanda bazata iya ganin laifinsa akan abinda maifinsa ya aikataba saida kuma batajin zatabar jinin duk Wanda ya zuba ya zube a banza sultan abdulshams zai dandani kalar nata rashin imanin. Juyar da idanuwanta tayi kan ammy dake tsaye tana kallonta da idanuwanta dake bayyanarda tsananin damuwa da tashin hankalinda take ciki. Ajiyar zuciya tasauke ahankali idanuwanta na cikowa da hawaye sbd itace ta rasa iyayenta,itace baiwa a dah,itace uwar da aka kashewa 'da tun kafin tafita daga radadin naqudarsa data wuni tana saidai ba itace abin tausayiba sune abin tausayin sbd yanda take jin zuciyarta dakuma sanin abinda ya samarda karagar mineelik batada tabbaci akanta da abinda zata iya yi sbd wani irin fushi,xafin zuciya, qunci,rashin tausayi da bushewa takeji a zuciyarta dan ita kanta ayanxu tasan tanada hadari sbd yanda takejin tamkar mineelik na cikin jikinta saidai soyayyar wainda take so da qauna tananan daram cikin ranta musamman shi daya zamo tamkar shine fitar numfashinta. Ahankali ta miqawa ammy hannu. Cikin tsananin farin ciki da 'doki ammyn ta qaraso ta zauna gefenta 'daya tareda kama hannunta cikin tsananin sanyin jiki tace, Rumanah ki....... Girgiza mata kai tayi ahankali ta bude baki tace, Ke uwace agareni kuma zaki cigaba da zama uwata ko wane irin mataki na taka,kome nazama bazan ta6a iya cutatardake ba laifin da aka sakaki kikayi koda badason rankibane wannan tsakaninki ne da ubangijinki bazanso wannan maganar tashiga tsakaninmuba. Kasa riqe hawayenta ammy tayi sbd kunyar rumanah ta miqe da sauri ta fice hawaye nabin fuskarta. Qoqarin maida kukanta takeyi saidai takasa sbd radadin datake ji mai zafi na mutuwar da iyayenta sukayi Da sauri ya rungumeta yanajin zafin ganin yanayinta tasaki wani irin kuka mai ciwo tana qanqamesa. Suhailat dake tsaye tanason yimata sannu da jiki ta juya ta nufi qofa jikinta amatuqar sanyaye zuciyarta na qoqarin jin zafi saidai tayi saurin kawar da hakan sbd ganin rumanar batada lafiya tana buqatar kulawarsa saidai duk yanda taso dannewa saida idanuwanta suka ciko da hawaye ta qanqame abeel ajikinta tana qara sauri dan isa gefenta. Baice mata komaiba saida tayi kukan iya yanda zuciyarta keso kafin tayi shiru tana sakin ajiyar zuciya ahankali. Dago fuskarta yayi yana kallonta ahankali ya shafota cikin sanyin murya yace, I love you ummu-rumanah bulama maheer abdulshams. Kallon cikin idanuwansa tayi akaro na farko dataji Kalmar na bata tsoro saidai tasan maheer 'dinta har abada bazai ta6a iya cutatar da itaba. Lumshe ido tayi ahankali ta bude tace, Ummu-rumanah nasonka tun kafin kace kanasonta saidai inason kayi min alqawarin zaka soni a duk halinda nashiga, Bazaka gujeniba, Kaine farin cikina soyayyarka itace qwarin gwiwata karka....... Hannunsa ya dora a bakinta yana mata wani irin kallo yace, Shihhhhhh get some rest now sbd gangar jiki da ruhi tare suke rayuwa tare suke barin duniya. Kallonsa tasakeyi tasaki wani irin numfashi mai sanyi tareda sake komawa jikinsa ta kwanta. Da kansa yakaita toilet tayi wanka ta fito tana duba closet dinta taga sabbin royal gowns 'dinda aka kawo mata ba adadi kowacce da kalar sarqoqinta nakai dana qafafu da hannuwa tareda wuya. Doguwar English gown tasaka har qasa mara hannu takallesa lokacinda yasake shigowa dakin ya riqo hannunta suka fito palonta na farko har zuwa dining inda aka jera abinci fiyeda kala biyar da mamaki take kallon dining din sbd ganin duk girmansa ancikasa da kalolin abinci da fruits ga masu tsaronta mata da aka kawo tun daga palonta na farkon shigowa har wannan din sai wasu irin samudawan guards da aka zuba tun daga qofar part din dazagayensa har zuwa hanyar dazata rinqa kaita zuwa fada. Kallonsa tayi yasakar mata wani murmushi ahankali tareda jawo mata kujera ta zauna tana kallonsa fuskarta daukeda qaramin murmushin qarfin hali sbd har lokacin zuciyarta cike takeda radadi sosai takejin kamar ana babbaka jinintane ana qunarsa mai laifi kadan take nema ta dau mataki akansa saidai kasancewarsa tareda ita yasa take iya control din yanda takeji saidai kamar abin nason yafara mata yawa. Cikin nutsuwa sukaci abincin duk da kadan taci tasha maganinda aka aje kan dining din daga negasi. Harsuka gama cin abincin idonsa nakanta sbd sosai ya lurada sauyi atareda ita saidai zuciyarsa naqara jaddadawa kanta arayuwa babu abinda zai rabata sonta. Kasancewar bata fara sallah ba yasa yakaita daki yasake kwantar da ita ya zauna tareda riqo hannunta cikin nutsuwa yace, Inason sanin abinda yafaru tsakaninki da ammy. Kallonsa tayi kafin ta dauke kai tana sake sawa zuciyarta qin ganin laifin ammyn kai tsaye tace, Sultan ya kashe iyayena da taimakon ammy da jakadiya. Cikin wani irin mugun yanayi na mamaki yake kallonta Ta zame ta sauka gadon ta nufi bakin window ta tsaya. Gabanta ya zagayo ya tsaya yana kallon cikin idonta ta rintse idon tana dauke kai. Ahankali ya bude baki zaiyi magana ta bude idanuwanta dasukai ja ta katsesa cikin sanyin murya da cewa, Bana maka wani kallo na daban a zuciyata bayan Wanda nake maka na mahadinta ko Allah baya kama wani da laifin wani.... Shiru tayi tana tauna Kalmar dazata fada cikin qarfin hali tace, Na yafewa ammy sbd Allah da soyayyarta gareni da kasancewarta mahaifiya kuma kaka ga mutane biyu danafiso ayanxu fiyeda rayuwata dakomai,kai YARIMA MAHEER ABDULSHAMS da ABEEL HASSAN...... Cikin sanyin murya dake nuna baqin cikin dayake ciki ya furta, Sultan f.... Bai qarasaba tace, Kayi hakuri. Ta juya masa baya cikin wani irin zafi datakeji a zuciyarta ta rintse ido tasake cewa, Kayi hakuri. Kasa motsi yayi sai idanuwansa dasukai jajir yana jujuya kalmarta ta yayi hakuri....zata dauki mataki akan mahaifinsa kenan.... No not possible...tokuma ko Ba itace akan mulkiba tana buqatar justice..... Ficewa yayi sbd jin kamar numfashi na masa wuyar ja ko gani sosai bayayi sbd tashin hankalin dayake ciki. Suhailat dake tsaye gaban windonta taga fitowarsa daga sashen na rumanah ta 'dauke kai tareda barin jikin windon sbd gujewa ganin damuwa. Yana fita ta zauna bakin gado tareda dafe kanta ta rintse idanuwanta kanta na mata wani irin ciwo. Koda dare yayi duk yanda taso bacci kasawa tayi sbd kewar iyayenta da 'yayanta. Koda gari ya waye qarfe goma wata zungureriyar takardar saqo daga alqalamin sauraniyar mineelik ummu-rumanah bulama ta isa hannun sarkin fada haroun inda saqon yake cewa ayau angama karbar duk wani bayani akan asalin sarauniya ummu-rumanah daga baiwa mamani dan haka ayau za'a yanke mata hukunci. Atake aka buga sanarwa koina ya dauka qarfe goma sha daya jama'a suka taru ana jiran isowar assultana. Cikin wata irin royal gown tafito red mai adon golden gashinta koina rufe da adon sarqar farin zinari wasu irin samudawan guards ne maza da mata taredasu Jakadiya a bayanta ta fito suka nufi fada. Cikin nutsuwa na wani irin miskilanci ya yasha gabanta yana kallonta guards din bayanta suka nufosa ta 'daga musu hannu tareda juyowa cikin nutsuwa ta kalli Jakadiya tace, Duk Wanda yasake gangancin tare mijina aduk lokacinda yakeda buqatar magana dani yana ganganci da rayuwarsane a sanarda kowa. Cikin tsananin ladabi dukkaninsu suka sauke kai suna tuba. Ta juyo ta kallesa cikin nutsuwa tace, Ina kwana? Kallonta yayi kafin ya watsawa su jakadiya wani mugun kallo atake suka ja baya sukai 'dan nesa kadan dasu. Ya kalleta cikin ido yace, Bazaki yankewa mamani hukuncin kisaba that's an order amatsayin na mijinki Ba mamaniba har kowama bazaki yankewa hukuncin kisaba nin...... Sultan ne bakason a kashe ba mamani ba"""ta fada tana kallonsa cikeda fargabar abinda zaice. #mamuhgee Sorry manage. [8/3, 7:40 AM] ummul aulad: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *40* _Not edited_ Kallonta yayi yana sake kafeta da manyan idanuwansa ransa na qoqarin 6aci da zancenta zuciyarsa na qoqarin hana faruwar hakan ya bude baki zaiyi magana ya fasa ya kama hannunta da qarfi ya jata part din ammy dake kusa Tsakiyar palon ya saketa tareda kallonta cikin sautin dake nuna bacin ransa yace, Me kika fada yanxu? 'Dauke kai tayi kai tsaye tace, Kana qoqarin kare sultan ne akan laifukanda yariga ya aikatasu ne cikin son rai da ganganci saidai kuma nariga nayi alqawarin duk Wanda ya cutatar da wani sai anbi masa haqqinsa sbd wannan shine adalcin assultana,wannan shine banbancin mulkin son rai da adalci....duk Wanda ya kashe a kashesa wannan shine hukuncin a musulunce..... Riqota yayi da qarfi ransa na qarasa 6aci yace, Kina tunanin na hanaki hakane sbd sultan yana nahaifina? Kisa dai matuqar ina raye kuma da aurena akanki bazan ta6a bari kiyiba ko adama kin kashetane a lokacinda bana kusa da bazan taba bari ki kashetaba and da..... Qwacewa tayi tana kallonsa tace, Nice na kashe adama kana qoqarin cemin mai kisa ne???? Bayan kasan mutanen nan sun cancanci kisa tako wane sashe na sharia, Anyiwa iyayena kisan wulaqanci da son rai, Anyiwa 'dana kisar son rai da ganin dama duk basune masu laifiba nice danake shirin qaddamar da adalci wa kaina amma y....... Idan kina maganar abeel Hussain ne ni mahaifinsa nabarwa Allah duk Wanda keda saka hannu nabarsa shida ubangijinsa maganar iyayenki kuma amatsayina na mijinki nake baki umarnin kibarwa Allah bazaki qara yankewa kowa kisar wulaqanciba ki tabbatarda idan kika sake hakan ni maheer abdulshams mungama zama tare abakin aurenki gabak...... Cikin tashin hankali suhailat dake palon basusan da itaba tayi saurin katsesa da cewa, Abu abeel ka..... Shut up and stay out of this suhailat"""""yafada ransa a matuqar 6ace. Rumanah datai mutuwar tsaye tana kallonsa idanuwanta sun kada jajir suna zubo hawaye zuciyarta takai qololuwa gurin tashin hankali da baqin ciki ta bude baki cikin baqin ciki tace, Basaika datse alaqar dake tsakaninmuba nasan bana ranka ko gabanka kayi qoqarin barina da aurenka har zuwa yanzu da baka sallameni bayan haihuwataba sbd itace amfanina daman shiyasa kace haka sbd sanin sirrin zuciyata saidai........ Fixgoto yayi da qarfi zaiyi magana ta fixge jikinta tana sakin wani irin kuka mai qarfi da ciwo sbd zancensa ya girgiza duniyarta gabaki 'daya ya kasheta jitake zuciyarta kamar zata babbake ta kama da wuta sbd masifar dake ci mata zuciya. Cikin tsananin damuwa suhailat ta dauki abeel ta nufi palon qurya tafadawa ammy dake zaune cikin tunani abinda yake faruwa. Da sauri ta taso tana shigowa palon ya juya zai fice ammy tayi saurin riqo rumanah dake kuka kamar ranta zai fita takira sunansa ya tsaya cak batareda ya juyowa sbd qaran kukan dake sake hargitsa nutsuwarsa da tafasa zuciyarsa. Rungume rumanah tayi tana qoqarin rarrashinta saidai kukane takeyi sosai Wanda ke nuna tsananin ciwo da baqin cikin da zuciyarta ke ciki. Kasa tsayawa yayi ya rintse ido da qarfi ya fice yanajin baqin cikin kukanta da maganganunta. Suhailat dake tsaye ji tayi jikinta ya qara wani irin sanyi da kukan da rumanah keyi ahankali ta fice daga sashen sbd ganin suna buqatar tattaunawa tsakanin 'ya da uwa dan jin tayi tazama baquwa acikinsu su duka din har maheer 'din. Shiru ammy tayi da ita rungume a jikinta batareda tace mata komaiba sbd halinda take ciki tana buqatar tayi kukan ko dan ta rage nauyin dake zuciyarta, Maganar gskia ko ita bazataso rumanah ta zubar da jiniba sbd sauyi suke fatar samu daga gareta... Itace sarauniya ta farko a tarihin qasar gabaki 'daya data hau sarauta batareda jinin sarauta a jininta ba bama 'yar qasarba baquwar haure daga wata qasar, Qaddara ta koro iyayenta daga gida suka fada wani gari inda daganan Allah yasake jefasu hannun masu kamun bayi aka kamosu zuwa nan qasar aka haifeta amatsayin baiwa Wata qaddarar tasa ta auri yariman masarautar, duk wannan qaddarar data koro iyayenta ta zamtowarta cikin lissafin masu mulkin qasar ne wannan kawai ya tabbatarda akwai abinda Allah ke nufi da hakan Wanda suke fatar sauyine na alkhairi mezaisa suso ganinta tana aikata abinda sauran sarakunan suka aikata. Tasan tabbas maheer yayi hakan ne dan bazai iya bari ya rasataba dan idan ta cigaba da zubarda jinin karagar mineelik zata shiga jikintane sosai ta yanda zasu rasata har abada. Dakinta tashigarda ita ta kwantarda ita kan gadonta ta rufeta tareda shafa kanta ta fice taje palo ta zauna tareda kallon Jakadiya data shigo duba assultana jin shiru dan tuni aka zagaye sashen ammyn da tsaro kasancewar tana cikin. Dafe goshi ammy tayi cikin tsananin damuwa da rashin sanin mafita tace, Kije kisanarda sarkin fada haroun assultana ta 'daga hukuncin zuwa wani lokaci batajin dadi yanxu. Cikin girmamawa da jimami tace, To""ta fice taje ta sanar atake akai sanarwar aka watse tareda tsananta tsaro sashen ammy. Har dare tana sashen ammy kwance ko motsi bata yi tayi wani irin sanyi idanuwanta sunyi jajir. Shigowa ammy tayi cikin nutsuwa ta zauna bakin gadon tareda sauke numfashi ahankali cikin kulawa da sanyin murya takira sunanta. Bata motsaba ta bude idanuwanta dasuka kumbura batareda ta amsaba. Duk wani 'da na halak bazai iya kallon makasan mahaifansa ya qyalesuba matuqar yanada halin daukar mataki ko fansa akansuba.. Saidai kuma dangana da bariga Allah ta wata hanyar shine sasanci da kawo qarshe ga kashe kashen., Ummu-rumanah har abada haqqin asma'u da bulama bazai bar ko 'dayanmuba koda kin yafe mana saidai kuma ina sake roqon yafiyarki a maimakon mu duka 'din, Wlh rumanah ina kallonki amatsayin 'yar dana haifa, Ina qaunarki da sonki har cikin zuciyata fiyeda wasu daga cikin 'yayan dana haifa shiyasa bazan iya bari naganki cikin wata muguwar rayuwa. Kisan bashine mafitaba bashine zaisa kiji sanyi a mutuwarsuba saima lalata rayuwarki dazakiyi ta hakan sbd har abada bazaki yafewa kanki abinda kikayiba zaki tsinci kanki cikin baqin ciki da damuwar da muma muke ciki ayanxu, Mijinki yana miki sonda bazai iya bari ki fada wani mummunan haliba bawai yanayi ne dan karki kashe mahaifinsa saidan yana tsoron hakan zai qarasa gusarda imaninki ne. Amatsayina na uwa ba sultana matar sultan mahaifiyar maheer ba nake baki shawarar karki kashe mahaifin mijinki ki bar iyayensa da haqqin ran iyayenki wlh Allah zai kamasu sbd baya taba barin haqqin wani akan wani dan haka kiyiwa magana nazari. Miqewa tayi jiki asanyaye tabar dakin tana fatar rumanar tayiwa zancenta kyakkyawan fahimta. Qofar da ammy ta fita ta qurawa ido idanuwanta nasake kadawa sbd zancen ya shigeta saidai fadanta da maheer ya kasa barin zuciyarta ta nutsu da daga bakinsa wainnan kalaman suka fito tabbas zuciyarta bazata tsaya wasi wasin daukarsu ba,, Meyasa zai fada mata kalaman dasukafi dalma zafi gurin tarwatsa kunnuwanta da zuciyarta????? Meyasa zaiyi fushi ya iya furta mata kalaman rabuwa da ita bayan alqawarin dayayi mata badan mutuwaba dashi da ita bazasu rabeba???? Wasu irin hawaye masu radadi suka gangaro mata ta rintse ido tana qoqarin danne kukan dake qoqarin zuwar mata. A cikin daren takoma sashenta tareda guards inda ta bada gargadi mai qarfi akan batason ganin kowa. Kwana biyu tayi bata fito ko qofar part dinta ba.. Abincin safe rana dare haka ake kwashesa bata fitowa saidai ammy tazo dakanta har bedroom tasata cin abinci dole. Duk iya yanda take jin kewa da soyayyarsa na cin zuciyarta dannewa tayi sbd har lokacin zuciyarta cike takeda zafi da radadin kalamansa shima kwana biyun bai nemeta ba hakan yaqara quntata yanayinta. Nuratu data rungumi qaddara da hannu bibbiyu akan mahaifiyarta still itace ke kulada rumanar amintacciyar baiwarta duk da da farko anso hanata ko kusantar inda rumanah take saidai rumanar ta hana sbd tasan suna tsananin buqatar juna sbd sukadai suke ganin junansu amatsayin jininsu tunda mamani sunanta matacciya. Sultan kuwa a rubuce ta aikawa harooun da takardar a tsananta tsaro a sashensa kowama yanxu ta hana yashiga gurinsa Hakan kuwa akayi nan take aka cika umarninta tareda bada gargadi ga duk Wanda yaje kar abari yashiga. Kwance take kan doguwar royal chair 'din shaqatawa dake qaramin palonta dakeda manyan qofofi guda biyar dasuke ta bayan garden din shashaqatawarta, A rufe idanuwanta suke saidai Sam ba baccin takeba iskar gurin mai sanyi take kado mata ta shara sharen labulayen winduna da qofofin palon dan ragewa kanta zafi da quncin datake ciki. Ahankali ta jiyo kukan jariri na shiga kunnenta ta bude idanuwanta a hankali sbd tasan kukan abeel ne tunda kaf masarautar babu jariri bayanshi. Tashi zaune tayi cikeda kewar 'danta da tausayinsa na rashin 'dan uwansa dakuma 'dumin jikin mahaifiyarsa Miqewa tayi ta nufi qofar bakin window ta tsaya tana hango cikin bedroom din suhailat da itama ta iska ke daga farin labulenta.... Rungume take dashi a tsaye tana jijjigasa cikin tsananin kulawa da damuwar kukan nasa Ta 'dagosa tafa duba fuskarsa cikin qaunarsa tayi kissing kumatunsa tana cewa, Abeel please kayi hakuri mummy bazata sake baka maganin zazzabi ba kaji pls my little prince forgive mummy...... Hawayen datake ruqewane suka gangaro mata na tsananin soyayyar 'danta da qaunarsa saidai kuma bazata iya karbarsa daga suhailat na.... Tunda ta shigo rayuwarta ta sanadinta ta rasa komai, Ta rasa jin dadi,kwanciyar hankali da soyayyar mijinta sbd ita, Ta rasa babynta sbd jin mijinta ya aureta, A yanxuma ta rasa jemal ne sbd ita Dan 'yayanta akaso kashewa duka tsautsayi yasa aka kashe mata jemal kuma gashi ta rasa mahaifarta har abada... Gashi ta riqe 'dan kishiyar datai sanadin rabata da komai da zuciya 'daya tana qaunarsa tamkar itace ta haifesa,,, Wace irin soyayyace takewa maheer??sbd tasan tana tsananin qaunar abeel ne sbd shi 'din tsotson maheer ne. Idan suhailat ce a matsayinta na yanxu zata iya kashe mahaifin maheer? Duk wainnan abubuwan da suhailat ta rasa ta dangana bata riqe kowa araiba gashi tana rayuwarta gwargwadon iyawarta batareda tasaka damuwar duk Wanda ya cucetaba koya tauyeta.....meyasa ita takasa hakan? Suhailat tafita son maheer ne??? Girgiza kai tayi tareda durqusawa a gurin tana zubarda sabbin hawaye masu radadi da ciwo gabaki 'daya ta rasa nutsuwarta da sukuninta rashinsa atareda ita jitake tanason zubarda jinin duk Wanda ya cutatar da ita da iyayenta da 'yayanta SBD kalamansa dasuke yawo cikin kanta suna qona zuciyarta... Cikin kuka tace, Bakasan rashinka taredaniba ha'darine dan zan iya aikata abinda bakason dan Allah kadawo gareni maheer. Suhailat data shigo palon dan kawo mata abeel tagansa sbd ta hangota lokacinda take kallonsu tayi saurin tsayawa cak jin abinda rumanar tace. Numfashinta taji yaqara gudu tayi saurin juyawa dan ficewa tun kafin rumanar taganta Saidai tana juyowa tagansa tsaye bayanta idanuwansa sunyi wani irin zurfi ya qureta da ido. Tsawon kwanaki kenan itama bata sakashi a idoba 6acin ran rumanah duk yashafesu saidai Sam bata damu sosai da rashin ganinsaba sbd tasan irin radadi da zafi da zuciyarsa ke ciki na fada da abinda kafiso fiyeda komai. Rabasa tayi zata fice sbd ahankali ya kira sunanta ta tsaya cak Rumanah kuwa tun shigowarsa taji qamshinsa saidai bata juyoba sbd wani irin bugawa da zuciyarta keyi. Hannu ya miqa ya dawo da suhailat gabansa cikin murya mai bada umarni yace, Miqa mata 'danta. Arikice takallesa itama rumanah a firgicen ta juyo takallesa. Fuskarsa a matuqar 'daure yace, Kibata 'danta. Wasu irin hawayen soyayyar abeel da qaunarsa suka gangarowa suhailat takalli abeel din takalli fuskar maheer din taga babu sakewa ko kadan ta juya tana tsiyayar hawaye qafafunta na rawa ta nufi rumanah datai mutuwar tsaye cikeda mamakinsa. Siririn kuka suhailat tasaki tareda 'daga hannuwanta ta miqawa rumanah abeel. Cikin rawar murya rumanah ta bude baki daqyar tace, Nabar miki shi. Girgiza mata kai suhailat tayi tana wani irin kuka mai ciwo da qaramin sauti. A firgice tasake cewa, Wlh na barmiki shi.... Girgiza mata kai suhailat tasakeyi tareda ajiye mata shi kan kujera ta nufi qofa da gudu tana toshe bakinta sbd kukan dayaci qarfinta. Dawo ki daukesa. Cak ta tsaya tareda juyowa takallesa da sauri Ki daukesa nabakishi bar abada 'dankine. Da sauri tadawo ta daukesa ta rungume tareda dawowa gaban maheer din ta rungumesa cikin tsananin farin ciki tace, For a moment I thought na rabu da abeel har abada..nagode. Kallon rumanah data zuba masa ido yayi cikin kulawa yace, Suhailat idan babu so biyayya na jawo soyayya fiyeda komai, Idan akwai so rashin biyayya na rusashi komai qarfinsa.. Har abada suhailat matsayinki daban yake cikin zuciyata bazan ta6a daina ganin girma da qimarkiba. Sanyi jikinta yayi masifar yi sbd gane amfani yayi da ita gurin isarda saqo ga rumanah... Wani irin ciwo da radadi taji yana tasowa a zuciyarta akaro na farko data kasa riqe abinda yake zuciyarta tasaki wani irin kuka mai ciwo tareda ficewa tana dafe qirjinta dayake mata zafi sosai. Gabanta ya qaraso ya tsaya yana kallon cikin idanuwanta dake zubard hawayen abinda yayi yanxu dan ta tabbarda ita yake fadawa magana bada suhailat din yake. #mamuhgee. [8/5, 5:22 AM] ummul aulad: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *41* _Not edited_ _*Marubucin gskia baya rubuta abu acikin labarinsa batareda yayi bincike ko tambaya ba yayiwa abin cikakken sani kusani marubuci ba jahili bane sbd wata tambayar ko comment din tamkar wanka da jirwayene akewa marubuci dan haka kusani ni bana rubuta abinda banida sani akansa.*_ Juyawa tayi tabasa baya zuciyarta na wani irin bugu sbd zafin maganar daya gama fada mata, Kobai fadaba tasani yafi ganin girma da qimar suhailat sbd ko babu komai itace uwar 'yayansa kuma macen data girmama dukkanin abinda zaizo mata dashi saidai tasan itama baza'ace bata masa biyayyaba,,,, Rintse idanuwanta tayi zuciyarta na sake jiyo mata zafin abin, Da kishiyarta yake gaya mata maganar bata masa biyayya...sabon ciwon hakan taji ta rintse ido da qarfi tareda girgiza kai ta juya ta nufi qofa tana qoqarin maida kukanta. Riqo hannunta yayi daidai lokacinda tazo wucesa ya dawo da ita gabansa yana kallon fuskarta data qi kallonsa saidai yanayinta ya nuna jin zafinsa ne cikin ranta. Kujera ya nufa ya zaunar da ita ahankali kafin shima ya zauna tareda riqo hannunta cikin nutsuwa da kulawa yace, Kina tunanin wannan itace mafita??? Kina tunanin a halinda muke ciki yanxune lokacinda yakamata mu ringa samun matsala akan abinda nake  buqata nakuma baki umarni?.... Kina tunanin sbd kare mahaifina nakeson dakatar dake daga abinda kike shirin aikatawa??? A musulince duk Wanda ya kashe a kashesa amma idan kashewar zata kawo kashe kashen bayin Allah da basujiba basu ganiba to an yarda abar Wanda yayi kisar sai ayi masa wani hukuncin kwatan kwacin zafin abinda ya aikata. Kina tunanin sultan mahaifanki kawai ya kashe? Sultan ya bada umarni ankashe mutanen da sukafi mahaifanki abin tausayi, Ya maida yara qanana marayu babu adadi, Ya saka mata zaman takaba babu adadi, Duk kina tunanin yin kansa ne kokuma ra'ayin kansa ne??? Dana barki da tun a shrkaran jiyar kinzama abinda yafi sultan ha'dari dan kuwa da yanxu jinin mutanen da kika zubar yafara ta6a qwaqwalwarki... Kinga abinda mu bamu ganiba labari kawai mukeji na asalin abinda ya faru har aka samu karagar kuma kinsan duk wata masifa dake bibiyar masarauta nan har yau ankasa samun Wanda zaiyi amfani da tunani da baairarsa domin kawo sauyi domin kuwa tun farko kisar cin amana ce ta samarda karagar kuma har yanxu kisar ce akeyi kina tunanin hakan shine mafita da sauyi tareda jin qan da talakawan qasar ke buqata bayan sune ake kashewa wainda basujiba basu ganiba., Kinason yankewa sultan hukuncin kisa bawai dan fadar musulunci ba saidan daukar fansar kisar iyayenka Wanda hukuncinki kwata kwata baiyiba a musulunce sbd kai tsaye fansa ne kika dauka,, Kafin sultan anyi kashe kashe da dama wainda ma sukafi nasa dan haka... Ina sonki bazan iya bari kibi hanyar da sauran sukabiba, Bazan iya bari rayuwarmu ta lalace ba sbd rayuwata zata lalace ne daga lokacinda taki ta lalace dan haka bazan iya bariba, mahaifina tun tuni naso na kubutardashi daga hakan amma yayi aiki da qarfinsa na zama mahaifi agareni ya nesantani da kansa dan haka bazan sake aikata wannan kuskuren ba sbd ke din ikona ce. Na auri suhailat shekaru shida zuwa bakwai yanxu..., A cikin shekaru bakwai dinnan bantaba fada suhailat ta fadaba sbd soyayyarta gareni mai girma ce irin girmanda yake sakata shanye duk wani tauyewa dazai fito daga gareni., Kece rayuwata,kece abinda zuciyata tafiso fiyeda komai saidai gaskiyar maganar shine suhailat itace nutsuwata......itace mace mafi girma da qima a idanuwa na bayan mahaifiyata... Rintse idanuwanta tayi da qarfi zuciyarta na tsananta bugawa jikinta na daukar rawa hawayenta na tsananta. Kallon yanayinta yayi cikin damuwa yace, I can't lie to you amma steps dinda kika fara son dauka sun fara ankarar dani babban kuskuren danake shirin aikatawa na barin suhailat ta fita daga rayuwata and idan kika cigaba da qoqarin binsa to tabbas zaki rasani...... Wani irin kuka ta fashe dashi mai qarfi da shiga zuciya tareda zamewa qasa ta zauna ta cusa kanta cikin qafafunta tana jin sabon nauyi cikin zuciyarta sbd dukkanin rayuwarta ta hargitse ta juya ta zama wani abu na daban, Tana tunanin zatayi rayuwar aure mai dadai saidai gabaki dayama rayuwar auren data kowama ta lalace tun haihuwarsu masarautar ta hargitse takoma gidan baqin ciki sbd kowa yarasa gane inda aka dosa. Dafata yayi ahankali tareda furta, I love you queen ummu-rumanah bulama, Ina sonki zanci gaba da sonki har numfashina na qarshe. Miqewa yayi ahankali yabar dakin idanuwansa na qara kadawa zuwa jajir. Sabon kuka tasaki bayan fitarsa tanajin maraici da baqin cikin wainda sukayi sanadin barowar iyayenta da gida har sukazo nan aka haifeta..wace irin rayuwa tasamu kanta ne aciki.. Tabbas tanason yankewa sultan hukuncin kisa ne badan ya cancanta ba sai dan daukar fansar kisar dayasa akayiwa iyayenta, kwata kwata zuciyarta takasa yarda tayi masa hukunci akan dukkanin abubuwan dayayiwa bayin Allah kanta kawai da iyayenta take gani Wanda idan tayi masa kisa akan hakan sun zamo daya babu banbanci a tsakaninsu. Kuka takeyi sosai tanason ko nauyin dake danne da zuciyarta ya sauka amma saima wani sabon qunci dake qara mata nauyi. Kuka takeyi sosai tareda dafe zuciyarta dake mata tsananin radadi da ciwo, Kukan datakeyi ayau yafi na ko yaushe sbd duk wani hope datake dashi akan zai sota wata rana ya rusashi dan kuwa ta tabbarda zuciyarsa ba ita takesoba kuma bazata ta6a sontaba. Taso ta zauna dashi har qarshen rayuwarta sbd qaunarta garesa mai girma da tsafta ce saidai kuma hakan bamai yiyuwa bace sbd tasa zuciyar takai qololuwa gurin son wata Saisai Bazataga laifin rumanah ba sbd tun kafin aurenta tasan babu soyayyarta a zuciyarsa saidai qauna da girmamawa zuciyarta ta dauki wannan sbd babu wata a zuciyarsa tana fatar tashiga wata rana saidai yanzu dayakeda wadda yakeso rayuwarsu su duka na neman lalacewa sbd soyayyarsa dan haka yau duk wani abinda takeson tabbatarwa ta tabbatar dan kuwa har abada bazai ta6a sonta tunda bai sota sbd 'yayanta da shekarun dasuka diba ba. Ahankali ta tsaida kukanta saidai hawayenta dasuka kasa tsayuwa cikin muryar kuka da tsananin karaya tace, Ka tarwatsa duk wata soyayyarka dake raina maheer. Kallon abeel dake kwance tayi tabbas tana qaunarsa saidai bazata rayu dashiba dan kuwa zama a tsakanin iyayensa ya qare mata har abada. Hawayenta dasuka kasa tsayuwa ta share tareda miqewa ahankali ta nufi wardrobe dinta ta bude. Ahankali ta fidda dukkanin kayanta ta hada na abeel tareda duk wani abinsa dake gurinta. Acikin daren babu Wanda yayi bacci acikinsu sbd babu Wanda yake cikin nutsuwa kowannensu tunanin step 'din dazai dauka dan kawo sauyi arayuwarsa mai kyau yakeyi. Suhailat tagama yanke shawarar rabuwa dasu takoma qasarta sbd tabbas kota cigaba da zama zaman takurawa juna zasucigaba dayi musamman yanzu dayake buqatar lokacinda zai daidaita komai na masarautar ta hanyar matarsa dan haka tafiyarta shine mafita ga dukkaninsu gabaki 'daya. Tsaye yake bakin windon palon sama na gidan khaleefa ya qurawa waje idanuwansa dake cikeda rashin bacci da damuwa.. Khaleefa dake zaune yana kallonsa cikin tsananin kulawa yace, Kaine shugaba kuma kaine haqqin kawo gyara acikin zamanka da matanka ya rataya akanka., Tun farko kaso kawo gyara batareda ka hau ba Allah bai nufa ba sbd lokacin yanke ijabar baiyiba amma yanzu lokaci yayi sbd Allah yabaka dama da ikon kawo sauyi ta hanyar matarka dake qarqashin ikonka itace sarauniya.... Saidai kuma saikayi taka tsantsan gurin gyaran sbd zai iya kawo rashin fahimta da matsaloli ga rayuwar aurenku musamman suhailat...... Juyowa yayi ya zauna ahankali tareda rintse ido damuwarsa na ninkuwa sbd sanin rayuwace zasuyi sarqaqqiya sbd har abada bazai hada soyayyar dayakewa rumanah da wadda yakewa suhailat ba sbd soyayyar rumanah a jininsa take tun haihuwarta.. Yanayin iya qoqarinsa gurin ganin bai tauye haqqin suhailat da 'yayansa ba saidai zuciya batada shamaki akan abinda takeso wani lokacin Wanda hakan yafara jawo masa tsana daga suhailat abinda bazai taba fatar yakasanceba. Dafasa khaleefa yayi cikin sanyin murya yace, Musulunci ya yardar maka da kasaki matarka idan har babu sonta a zuciyarka sbd gudun shiga haqqi dan haka zaka iya duba hakan sbd a yanxu bazata iya jure abinda ta jureba lokacinda take ita kadai.... Rintse ido yayi da qarfi jin wani irin zafi daya soki zuciyarsa da khaleefa yayi maganar rabuwarsa da suhailat. Miqewa tsaye yayi tareda nufar qofa ya fice batareda yace komaiba. Kai tsaye part dinsa ya nufa harya kai qofa ya tsaya cak. Juyowa yayi ahankali ya kalli qofar sashen suhailat da ake fita da akwatinanta. Ya saki numfashi ahankali cikin wani irin yanayi na damuwa sbd yasan za'ai hakan. Tabbas yana qaunar suhailat har cikin ransa kuma a shirye yakeda yin rayuwa da ita har mutuwarsa sbd abinda bata ganeba shine tanada wani matsayi mai girma a zuciyarsa na qima Wanda ko rumanah dayake so batadashi sbd ita zai iya rufe ido yayi mata wani abin amma bazai iya yiwa suhailat ba sbd akwai kunyarta mai girma a idanuwansa saidai bazai tilas ta mata ba ga duk abinda ta zaba akansa sbd ta cancanci abarta da abinda take raayi ayanxu. Juyowa yayi ya nufi sashenta a karo na biyu duk tsawon zamansu Wanda hakan na yasakasa jin wata sabuwar gagarumar kunyarta. Carolina ce a palo tana qoqarin fitowa da akwatinan qarshe wainda suke na abeel ne tana fitowa ta nufi sashen assultana dasu. Bedroom dinta ya shiga alokacinda ta dauki handbag dinta da abeel zata fito. Kallon juna sukayi dakyau Ganin yana qureta da kallo yasata sauke kanta ahankali tareda kwantarda abeel ta 'dago ta qura masa ido ganin yanda duk ya rame lokaci 'daya yayi wani irin canzawa saidai kuma abin tausayin shine yana cikin wannan halin ne sbd halinda rumanah take ciki. Gangarowa hawayenta sukayi ta sauke kai ahankali cikin sanyin murya da nutsuwa tace, Ranar farko dana fara ganinka aranar nafara Sonka maheer ibn abdulshams abdallah,, Kaine namiji 'daya da zuciyata ke so saidai babban kuskuren danayi shine na nacewa na aureka a tunanina zaka soni wata rana saidai ashe babban kuskure da shishigi nayiwa qaddarar datake jirana.. Kallon cikin idanuwansa dasukai jajir tayi tasaki murmushi mai ciwo tace, Haryanxu ina sonka maheer abdulshams saidai bazan iya cigaba da zama dakaiba maheer sbd girman soyayyar danake maka bazanso zuciyata ta tsanekaba. Ayau ina roqonka sbd darajar 'Yayana da soyayyata ka sauwaqemin na samu rayuwar data cancanta dani wannan rayuwar ta gidanka ba tawa bace na tabbatarda tawa tana wani guri tana jirana. Rintse ido yayi akaro na farko dayaji ruwa sun ciko idanuwansa sbd ita ya girgiza kai yanason magana amma yakasa. Ta riqo hannunsa tana qoqarin maida hawayenta tace, Wlh idan nacigaba da zama dukkaninmu zamu cutu qarshe dukkaninmu zamu fada hanyoyinda bazasu amfanemu ba sbd zan iya canzawa na zama wata daban, Canzawata zatasa ka tsaneni Tsanata dazakayi zaisa matarka ta canza sbd zata riqa ganin itace abar so nikuma zata riqamin kallon mahaukaciya qarshe dukkaninmu zamu zama abinda bama fatar kasancewa... Na yarda da aurenka shine qaddarata kuma na karbeta da hannu bibbiyu kuma ina fatar Allah yasa na cinye wannan jarabawar zuwa yanxu sbd zuciyata tafara gazawa dan haka nake roqon alfarma ta qarshe daga gareka dan Allah free me from this relationship Wlh I'm in so much pain zuciyata zata iya bugawa kowane lokaci please free me maheer. Girgiza kai yayi yana kallonta da idanuwansa dasuka canza daqyar ya iya furta, Suhailat I need you in my life please don't..... Girgiza kai itama tayi kukanta na qoqarin qwacewa tace, Wlh bazan iyaba maheer, Wlh mutuwa zanyi I've endured enough, Duk abinda kamin na yafe maka ina fatar kaima ka yafemin goodbye yarima maheer abdulshams. 'Daukar abeel tayi ta rungume wani irin ciwo mai zafi nacin zuciyarta ta rintse ido hawaye masu zafi suka gangaro mata tasaka hannu ta goge fice dakin. Kodata fita palo Carolina da sauran masu hidamarta duk suna tsaye kowanne idanuwansa cikeda hawayen rabuwa da ita. Kallonsu tayi tareda sakin murmushin qarfin hali ta fice sbd bazata iya cewa komaiba ta nufi sashen rumanah. Zaune take a palonta tayi lamo ko motsi batayi ta qurawa gefe 'daya idanuwanta dasukai jajir suka bushe dukkanin wani abincin karyawa an Jere mata a gabanta saidai ko motsi batayiba bare takalli abincin gashi har rana tafarayi, Ganin halinda take ciki yasa dukkanin masu hidimarta da masu tsaronta yau jikinsu asanyaye yake ko babban motsi ba'ayi a sashen tsit kakeji. Da shaqaqqiyar muryarta datasha kuka tai sallama tashigo palon taganta zaune da alama agurin ta kwana tun jiyan sabd ganin kayan jikinta. Ahankali taqaraso gabanta ta durqusa ahankali ta dora mata abeel ajikinta. 'Dago idanuwanta tayi a wahalce ta kalleta takalli abeel ta tashi zaune daidai tareda qurawa abeel 'din ido ta 'dago takalli suhailat ahankali ta iya bude baki sbd tsananin nauyi da ciwon kan datakeji tace, Shine da kansa yace yabaki bayan nima nace nabar miki sh...... Nagode sbd kema kinyi abinda bakowace uwace zata iyaba ciki hardani kuwa sbd bazan ta6a iya bawa kowa 'dana dana haifaba, Ina qaunar abeel qauna mai tsafta sbd shi 'din 'dan maheer ne kuma ina kallonsa amatsayin jemal dina dana rasa saidai zamansa hannuna bamai yiyuwa bane Allah ya albarkaci rayuwarsa. Juyawa tayi ta nufi qofa ta fita batareda tasake cewa komaiba sbd batason bayyanarda hawayenta gaban rumanah tabarta da jin cewar kamar itace silar rabuwarsu. #mamuhgee [8/6, 1:17 PM] ummul aulad: _*TARAYYA*_ _wattpad@muhgee_ _Haske writers association_💡 *42* _Not edited_ Kasa motsi tayi tabi bayanta da kallo harta fice ta jima tana kallon qofar kafin ta maido kallonta kan abeel daya farka yana kallon fuskarta ta rintse ido tareda rungumesa tana jin wata sabuwar damuwar sbd rashin sanin abinda yafaru yanxun. Ahankali ta lumshe idanuwanta mafarkin abbanta datai yau yana dawo mata. "Ummu-rumanah kibi mijinki a dukkanin umarninsa matuqar basu saba addininki ba sbd shine gatanki kadai yanxu aduniya, Ki gujewa mulki sbd haqqoqin dubban mutane da bazaki iya daukaba sbd rauninki na zamowa 'ya mace kibarwa Allah komai ki gyara aljannarki.""" Kalaman da mahaifinta ya sanarda ita a mafarki kenan saidai abinda takasa ganewa shine ta yaya zata sauka mulkin batareda ta kawo sauyi da zaman lafiya a qasar ba. Bude ido tayi tareda jinjina shawararda zuciyarta ke bata dan kawo qarshen komai saidai hakan wani abune mai girma dayakeda matuqar hadari saidai dole zata aikata hakan koda hakan shine ajalinta zatayi dan kawo qarshen rayuwar da alummar qasar suka samu kansu. Tabbas qaddararta itace ta koro iyayenta daga gida ta kawosu nan sbd gashi abinda yafaru tun qarnikanda ko kakanninta ba'a haifa Ashe tana cikin qaddarar gashi itace zata kawo qarshen abin. Hawayen tausayin mijinta da 'danta tareda ammy ne suka gangaro mata ta sauke kanta tareda sakin kuka ahankali sbd tasan sune zasufi kowa kukan rashinta arayuwa sbd sune wainda takeda matuqar mahimmanci arayuwarsa ta yanda rashinta zai matuqar ta6a rayuwarsu. Sunansa ta furta ahankali cikin zuciyarta sbd tasan mutuwarta zata tarwatsa zuciyarsa zatabarsa cikin mawuyacin hali saidai tasan suhailat na nan zata kula dashi. Miqewa tayi ta nufi dakinta ta kwantarda abeel ta zauna gabansa ta qura masa ido tana fidda sautin kuka ahankali sbd kukane takeyi sosai. Tana fitowa sashen rumanah kai tsaye shashen ammy ta nufa bata nuna mata komaiba tasanarda ita zataje Mali. Ammy dake fama da ciwon kai mai tsanani takalleta da idanuwanta ahankali tace, Allah ya kiyayeki ya hadaki da alkairin dake cikin tafiyar. Amin ta furta ahankali tareda juyawa ta fice dan dama su amah suna Mali tuntuni da aka fara wainan rudanin. Motocin dazasu kaita airport na fitowa daga masarautar tasaki wani irin kuka ahankali tareda rintse idanuwanta tana furta Allah yabani juriya da danganar rabuwa dakai maheer. Suna isa airport basuyi minti ashirin ba suka tashi daga qasar Ethiopia zuwa mali. Lokacinda ta wuce tabarsa daqyar ya iya fita yabar dakin ya nufi part dinsa yana qoqarin danne halinda zuciyarsa ke ciki amma yakasa saida jiri ya zaunar dashi kan kujera da qarfi ya rintse ido ga mamakinsa saiyaji kamar hawaye na neman zubo masa yayi saurin dafe kansa da hannu bibbiyu jin kamar zai rabe masa sbd yasan bazai ta6a iya cireta aransa ba. Ahankali ta qaraso bayansa ta tsaya tareda zuba masa ido tana sake danne hawayenta.. Bude idanuwa yayi ahankali sbd he can feel her presence. Juyowa yayi suka hada ido atake takasa riqe kukanta tafara girgiza kai tareda sakin kukan Ya ware hannunsa 'daya alamar tahowa garesa da gudu ta qarasa ta fada jikinsa ya rungumeta sbd shikansa yana buqatarta kusa ayanxu. Kukan datakene yafara bashi mamaki ya 'dago fuskarta ya kalleta atake yaji kwanyarsa ta qarasa hargitsewa ya bude baki zaiyi magana tayi saurin 'dora bakinta cikin nasa tana tsiyar hawaye. Ahankali tasaki bakinsa tana kallon fuskarsa dake bayyane da damuwa cikin tsananin sanyin muryar kuka tace, Ina sonka yarima maheer abdulshams, Kaine farin ciki da rayuwar ummu-rumanah bulama, Kaine abinda zuciyata bazata iya jure rashinsa ba, Ina maka qauna mai girma a tun ranardana fara ganinka agabana., Wlh bazan taba iya aikata kuskurenda zai nesantani dakaiba bare kwatanta rayuwa babukai.. Kasan mutuwane kawai banyiba a daren ranar daka furta rabuwa dani maheer abdulshams, Ummu-rumanah bazata iya rayuwa babu kaiba sbd kaine jigonta kuma jagorarta.. Share hawayenta tayi tareda jan numfashi kukanta na rage sauti tace, Wlh haryanxu zuciyata zafi da takeyi da zancen daka fadamin kana tunanin zan iya rayuwane wlh mutu..... Maidata yayi jikinsa da sauri ya rungumeta yana girgiza mata kai dan bazai iya ko maganaba. Qanqamesa tayi tana cewa, Na tuba ka yafemin. Dora hannu yayi abakinta yana sake rungumeta ahankali ya furta, Maheer abdulshams loves you ummu-rumanah bulama., Ummu-rumanah bulama kece mahadin rayuwar maheer abdulshams. Murmushin qarfin hali tasaki ahankali tareda sake kwanciya ajikinsa. Shiru sukayi dukkaninsu ajiyar zuciyarta kawai ke fita akai akai Sai kuma shi dahar lokacin tunani da damuwar tafiyar suhailat ne kawai cikin ransa, Tana buqatar shan iska zai barta tasamu sarari idan yagama da matsalar mineelik ya tabbatarda rumanah ta fita daga cikin wannan masifar zaije yadauketa su koma Georgia gabaki 'dayansu. A daren ranar nan ta kwana gurinsa tareda abeel saidai kusan dukkaninsu babu mai nutsuwar yin bacci saidai shiru sukayi a kwance kowannen da abinda yake damun zuciyarsa. Washe gari koda aka tashi aka tararda Allah yayiwa mamani rasuwa Koda aka dudduba dan tabbatarda meya kasheta aka gano saran maciji ne har guri biyu a wuyanta da gefen hannunta sbd wani irin canzawa da fatarta tayi takoma Kore Kore alamar qarfin dafin macijin mai ha'darine. Lokacinda Jakadiya ta kawo mata saqon mutuwar suna zaune kan dining maheer na tilasta mata cin abinci. Kallon Nuratu dake jera musu sauran abincin breakfast din tayi da sauri tareda miqewa tsaye sbd ganin halinda tashiga lokacinda Jakadiya tagama fadar saqon da sauri suka rungume juna nuratu na sakin wani irin kuka ahankali tareda rintse ido tana girgiza kai. Hawayen tausayin nuratun ne itama suka ciko idanuwanta ta bubbuga bayanta cikin son daure kukanta dake zuwa na tausayin kansu sbd sun tabbata marayu iyayensu dasukazo nan suka haifesu sun rasu sun barsu ayanxu sune kadai 'yan uwan kansu. Cikeda tausayawa Jakadiya takallesu cikin sanyin murya tace, Allah ya gafarta mata laifukanta ya sadata da rahamarsa ina miqo ta'aziya ga assultana da 'yar uwarta nuratu akan wannan rashi. Ganin tana neman rikicewa da kuka yasashi yiwa Jakadiya wani kallo Atake tayi gyaran murya tana cewa, Nuratu kizo muje kiyiwa mahaifiyarki addua kafin a fice da ita. Sakinta rumanah tayi tareda kallon fuskarta tana hawaye tace, Allah yabaki haqurin rashinta yasakamiki dauriyar yimata addua. Kallon rumanar tayi sbd jin bata ambatarwa mamanin rahamar ubangiji ba ahankali ta bude baki cikin tsananin sanyin murya tace, Ina roqorwa mahaifiyata yafiya ki yafe mata sbd qauna da amincin dake tsakanina dake dan...... Kije na yafe sbd qauna da amincin dake tsakaninmu saidai haqqin ran 'yayana data dauka wannan tsakanintane da ubangijinsu shida ya haliccesu. Ahankali ta furta, ina fatar Ubangiji ya yafe mata. Juyawa tayi ta fice rumanah ta juya ta zauna tana qoqarin saita nutsuwarta kartayi kuka saidai Sam takasa sbd duk yanda mamani taqita takashe mata 'dah ita din tatace. Ta bayanta ya rungumeta jikinsa ahankali yana cewa, Sorry luv. Shigewa jikinsa tayi tana daina kukan dan tana buqatar rarrashin gabaki daya ta rasa ina ta dosa da rayuwarta. Jin tayi shiru yasashi shafa kanta cikin sanyin murya yace, Allah baya barin haqqin wani akan wani gashinan kin gani. Shiru tayi tana sauke ajiyar zuciya sbd tunowa da abinda zatai dan kawowa kowa sauqi da qarshen masifar sbd a yanxu abeel dintane kawai ake jira ya gia yahau dan haka bazata taba bari 'danta yahau wannan karagar ba sbd ajikinta tanajin masifa da balain dake cikinta yana yawo cikin jininta ita kadai tasan yaya takeji take daurewa sbd shirye take da yaqar komai akan qarfin soyayyar datakewa mijinta. Abu taji na fitowa ta hancinta ta taba ahankali tashafo taga jinine da sauri ta goge sbd kar Maheer yagani. Shigowar ammy yasashi sakinta suka miqe gaba dayansu murya a tausashe suka gaidata ta amsa tana kallon rumanah dataga tayi wani irin fayau kamar ba jini a jikinta ta tsaya gabanta tareda riqo hannunta suka koma kan royal cushions dake palon suka zauna tana kallonta cikeda mamaki tace, Rumanah ki fadamin gskia lafiyarki kalau? Gefen Maheer daya kafeta da ido ta kalla ta sauke kai cikin sanyin jiki tace, Lafiyata kalau. Girgiza kai ammy tayi tace, Rumanah wlh bakida lafiya wannan abun na cin jininki duba kiga kina canzawa rumanah karki rufeni kifadamin gskiar abinda kikeji. Dawowa yayi kusada ita ya zauna yana zuba mata ido cikin tuhuma ya riqo hannunta zai duba tafin hannunta ta zame hannun tareda girgiza kai tace, Lafiyata klau banajin komai.... Hancinta ya qurawa ido cikin daukewar numfashi yakai hannunsa ya shafo jinin dake gangarowa daga hancin ya kalla jikinsa na rawa ammy ma cikin tsananin tashin hankali take kallon jinin... Ganin suna kallonta tayi saurin shafowa taga jini sosai ta miqe tsaye wani irin jiri ya dibeta ta yanke jiki gurin ta fadi idanuwanta rufe jinin na sake ballewa daga hancinta. Cikin masifaffen tashin hankali sukayi kanta ammy tuni tafara kuka tana kiran sunanta Shikuwa daukarta yayi hankali amatuqar tashe yayi bedroom dinta da ita ya kwantar ya fidda waya atake yakira khaleefa dasu dr abeena tareda sauran manyan doctors nasu. Tissue yasa yana goge mata hanci saidai Sam jinin yaqi tsayawa gashi tafara wani irin jijjiga a rikice ya qanqameta jikinsa yana kiran sunayen Allah ahankali muryarsa na rawa dan yasan bazai iya kwatanto rayuwa babu itaba. A gigice dukkaninsu suka iso tareda nurses da duk wasu kayan aikinsu atake suka fara qoqarin tsaida jinin dan maqala mata oxygen sbd numfashinta daya fara mata wuyar ja. Dafasa khaleefa yayi tareda kallon yanda duk jikinsa ya 6aci da jini cikin kulawa yace, Kaje daga palo gurin ammy zakafi samun nutsuwar bari mu dubata. Palo khaleefa ya rakosa ya zauna kusada ammy yakoma ciki shi. Riqo hannunsa ammy tayi cikin tsananin damuwa da tausayinsa dana abeel dake rungume ajikinta tace, Zataji sauqi insha Allah. Jinjina mata kai kawai yayi sbd ko bude baki bazai iyaba bare magana. Atake rashin lafiyar assultana ya yada koina nan koina gari yafara 'daukar tsit sbd rufe shaguna da kasuwanni. Acikin masarautar kuwa Sam ba wani dogon motsi tako wane bangare sbd jiran tsammanin farfadowarta. Daqyar suka samu suka tsayar mata da jinin aka maqala mata oxygen tareda ruwa da sauran abubuwan da suka kamata amma har lokacin bata farfado ba. Bayan duk sungama abinda zasuyi aka bar nurses uku dan kulada ita suka fice. Lokacinda yashiga yaga yanda takoma lokaci daya Ya zauna bakin gadon tareda 'dora hannunsa kan nata ya rufe ido Shikadai yasan radadi da ciwon da zuciyarsa ke ciki ganinta ahaka. Ahankali yace, Tana farfadowa zamu wuce bazan iya zama anan ba kuma. Dafasa ammy tayi tareda yarda da abinda yafada dan itama tagaji da nan 'din tana buqatar nutsuwar rayuwa kota maida hankali gurin istighfar ga ubangijinta. Sai tsakiyar dare ta farka tareda bude idanuwanta ahankali ta qurawa masa ido yana zaune bakin gadon hannunsa cikin nata a damke idanuwansa a lumshe saidai tasan ba bacci yakeyiba. Ahankali ta bude baki da siririyar murya ta furta, Abu abeel.. Bude idanuwansa yayi da sauri tareda tashi zaune daidai yana kallonta fuskarsa na bayyanarda tsananin farin cikin daya shiga na ganinta. #mamuhgee. [8/7, 7:36 AM] ummul aulad: _*TARAYYA*_ _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association_💡 *43* _Not edited_ Murmushin qarfin hali tasaki tareda sake damqe hannunsa dake cikin nata tana kallon fuskarsa dashima ita yake kallo yana yiwa Allah hamdala cikin ransa. Tashi zaune takeson yi ganin kamar batada qarfin jiki yasashi tayarda ita zaune tareda cire mata cannula dake hannunta ya gyara mata zama sosai. Cikin sanyin murya da kulawa yace, Ya kikeji yanxu? Girgiza masa kai tayi tana kallon fuskarsa. Jakadiya ce tayi knocking qofar dakin ahankali ta sanarda zuwan sultana. Zare hannunta tayi cikin nasa tareda lumshe ido sbd yanayin datakeji ajikinta har lokacin. Cikin nutsuwa ammyn tashigo idonta kan rumanah din Hankalinta ya'dan kwanta ganin ta farka harta tashi zaune. Qarasowa tayi tareda miqawa maheer hannu ya kama hannun da hannunsa daya cikin nutsuwa yace, Ina kwana ya ammy? Murmushi tayi tace, Lfy klau..tana kamo hannun rumanah tace, Ya jikin? Naji sauqi ammy"""ta fada cikin qarfin hali da danne ciwon datakeji. Miqewa yayi ya fita yana amsa kiran khaleefa dake kiransa kan maganar test result 'dinta dasuka fito. Ammy dakanta ta kamata takaita toilet tayo wanka da brush tana fitowa taga doguwar riga mara nauyi akan dressing chair ta dauka tasaka ta shirya tana qoqarin busar da kanta sbd wankan tsarkin datayi na haihuwa ammy tashigo tareda nuratu dake daukeda babban tray Jere da breakfast ta ajiye zata juya rumanah takira sunanta ahankali. Tsayawa tayi tareda juyowa cikin ladabi Rumanah ta miqa mata hand dryer cikin sanyin murya tace, Taimakamin. Ammy na ganin hakan tasan magana zasuyi ta kalli nuratu tace, Tayi breakfast. Jinjina kai tayi alamar tou. Ahankali take busar mata da gashin babu Wanda yayi magana acikinsu. Tana gamawa ta daure mata gashin tareda ajiyewa a natse. Miqewa tayi itama ta nufi inda take sallah tana idarwa ta dawo kan couch din dakin ta zauna har lokacin nuratu na tsaye kanta a sunkuye cikin tarin damuwa da kadaici. Ahankali takamo hannunta ta zaunar da ita kusada ita ta kalli fuskarta kafin ta sauke kanta itama ta qurawa gabanta ido cikin sanyin murya tace, Kiyi hakuri nabarki alokacinda kike tsananin buqatata, Kin kuladani kin tayani kuka kin rarrasheni alokacinda na rasa nawa iyayen saidai ni nakasa miki hakan alokacinda kike buqatar wani ataredake.. Kallonta nuratu tayi hawayen datake riqewa suka gangaro mata tace, Wlh idan nace miki bana buqatarki ataredani na miki qarya rumanah saidai yanayin rayuwa daya kawo bambamci arayuwarmu ayanxu rayuwarki daban take data baiwar datafi kowace baiwa baqin jini sbd mahaifiyarta data..... Rintse ido tayi tareda budewa idanuwanta na cikowa da hawaye ta juyo ta kalleta cikin sanyin murya tace, Ada damuke bayi rayuwarmu tafi kwanciyar hankali da nutsuwa tareda dadin gudanar da rayuwarmu, Rayuwar bayi wata rayuwace mara yanci amma wlh wani lokacin tafi rayuwa irin wadda nasamu kaina aciki, Nuratu idan zaka roqi Allah abu ka roqi alkhairinsa sbd wlh rayuwata ina baiwa tafimin kwanciyar hankali akan yanxu. Gangaro mata hawaye sukayi sbd jin tausayin kanta da abinda zata fada tace, Nuratu na 'yantaki daga yanxu ke ba baiwa bace kinsamu 'yancinki, Babu wata rayuwar jin dadi da kwanciyar anan dan haka za'a maidaki gida acan zaki samu rayuwar kwanciyar hankali damukai burin samu idan ni bansamuba zan qoqarta gurin ganin ke kinsamu... Kallonta nuratu takeyi hawayenta na tsananta gudu tace, Tare mukayi alqawarin komawa gida..... Zanzo wata rana nima idan nauyin alummar dake kaina ya sauka Zanzo idan inada rayuwa da lafiya sbd burinane nima nahadu da dangin iyayena dan haka karkiyi wasa da damarki kice zaki jirani kije Allah zai sake sadamu da yardarsa. Kuka nuratu ta fashe dashi tana girgiza kai tace, Bansan ta yaya zan fuskanci mutanen da basusanniba nikadai nace musu dukkanin iyayenmu da sauran danginsu da akaje dasu sun mutu ba... Itama kukan takeyi sosai saidai bazata iya cewa komaiba sbd wannan shine gatan datasan zata yiwa nuratu takoma gida ta fuskanci sabuwar rayuwa cikin amincin Allah. Kuka sukeyi sosai na rabuwa da juna daqyar rumanah ta miqe ta bude wardrobe ta dauko wata jaka dake daukeda qatuwar sarqar zinari ta miqawa nuratu tareda juya mata baya sbd kukan datake riqewa tace, Allah ya hada fuskokinmu da alkhairi. Ta baya nuratu ta rungumeta tana sakin sabon kuka tana cewa, Kisani zan jira zuwanki har qarshen numfashina. Daqyar suka saki juna suka fito palonta na biyu inda suka tararda ammy da maheer da khaleefa tareda Jakadiya suna jiran fitowarsu. Fuskokinsu suka bayyanarda halinda suke ciki. Ya qurawa fuskarta datai jajir ido kafin ya dauke kai yanajin damuwar ganinta hakan cikin zuciyarsa. Gefen ammy ta qarasa ta tsaya ahankali ta bude baki tafada musu tafiyar Nuratu din zuwa qasarsu. Ammy sosai ta yiwa nuratu addua da fatan alkhairi tareda cewa jakadiya nuratun ta sameta kafin washe gari ta wuce. Bayan fitarta khaleefa yabi bayanta da kallo kafin maheer yayi masa magana da ido suka fita. Bayan fitarsu ammy ta zaunar da ita tasa aka kawo wani abincin breakfast din. A palon yarima maheer suka zauna cikin nutsuwa yace, Khaleefa zaka karbi duk wani bayanin tarihin my queen da mahaifiyar nuratu ta bayar ka kaita har gida kafin ka karbi takardun iyayenta kayi amfani dasu ka nemomin asalinta. Shiru khaleefa yayi yana sake tauna zancen sbd tafiyar ta jirgin ruwa ce sbd ta ruwa kawai zasubi su bulla garinsu nuratun kai tsaye a yanda akace gashi bai cika son tafiyar ruwa ba saidai kuma dole haka zai daure saidai suyi amfani jirgin dazasu isa cikin kwana biyu. Acikin daren rumanah tayi kukan tafiyar Nuratu, Iyayensu sunzo qasar dasu acikinsu gashi su zasu koma batareda ko dayansuba. Washe gari bayan sallar asuba suka wuce bayan khaleefa yakarbi duk wani tarihi na asalinsu daga hannun anees mai haqqin tattara tarihin sarakunan masarauta Wanda aka ya karbi bayanan daga mamani ya rubuce a littafin tarihi kafin rasuwarta. Bayan tafiyarsu takira Jakadiya ta miqa mata wani zungureren saqo a rubuce tace takaiwa harooun sarkin fada. Lokacinda Jakadiya takaiwa harooun saqon yana gama karantawa jikinsa yayi matuqar sanyi da abinda ke rubucen saidai kuma yasan hakan datake shirin yi shine qarshen abinda yake bibiyar mineelik dan haka babu bata lokaci ya fita dakansa yaje gurin Negus sarkin qirar mineelik yayi masa bayani ya karbo littafin zanen karagar mulkin qarnikan baya yadawo yabawa jekadiya takai mata. Lokacinda Jakadiya takawo mata shirgegen littafin mai nauyi ko budesa batayiba tace, Kije na zabi lamba ta biyar. Babu musu Jakadiya takoma ta mayar tana jinjina alamarin rumanah sbd idan Allah ya taimaka abinda take shirin yi shine daidai. Acikin daren ranar Negus da yaransa suka fara aiwatarda aikin qera sabuwar karagar mulkin mineelik wadda basu ta6a qera abu mai kyau da darajartaba sbd abubuwan dasuka narka ana hadawa dasu gurin qirar. Lokacinda Jakadiya ta sanarda ammy abinda yake shirin faruwa numfashi ammy tasauke cikin danne fargabarta dan batason tunanin faruwar wani abin saidai zataje tayi magana da sultan sbd shine yasan komai ciki da waje gameda komai na karagar fiyedasu. Da daddare bayan ko ina yayi tsit sultana ta fito ta nufi sashen sultan kai tsaye aka barta tashiga sanin matsayinta gurin assultana. Zaune yake hankali kwance yana karatun wani shirgegen littafin tarihi yana shan madara mai zafi da aka kawo masa kullum kafin ya kwanta sbd tana qara lafiyar qwaqwalwa. Kallo daya yayi mata yasaki murmushi yana cigaba da abinda yakeyi. Qarasowa tayi kusadashi ta zauna cikin girmamawa ta gaidasa tana kallon littafin dayake karatu tace, Meyasa haryanxu bazaka sauke dukkanin wani tunani na sharrin shaidanba ka fuskanci gaskia ka bita, Ka tubarwa ubangijinka ka ajiye duk wata niyya da qudirinda bana alkhairi ba wlh Allah zai karbi tubanka sbd shi mai yafiyane ga bayin dasuka tubarmasa. Wani irin murmushi yasaki tareda rufe littafin ya ajiye gefe ya kalleta yace, Baiwarki kuma matar 'danki tayi babban kuskure na aikata abinda ta aikata sbd kaf tarihin mineelik babu wani sultan da aka taba muzantawa saini sultan abdulshams jinin ajani.... Numfashi tasauke cikin takaici da baqin cikin halinda mijinta yasamu kansa idanuwanta na cikowa da hawaye tace, Son zuciyar kakannin kakanninka shine yasamu ahalinda muka tsintsi kanmu aciki karka bari zuciya takaika aikata irin kuskurensu..... Katseta yayi da cewa, Meya kawoki ki fada kai tsaye sbd nasan akwai abinda yakawoki a wannan lokacin. Kallonsa tayi ganin Sam idanuwansa da zuciyarsa sun rufe.. Cikin sanyin murya tace, Assultana na shirin canza mineelik gabaki 'daya da wata...... Da sauri ya kalleta yana ajiye cup din hannunsa sbd girgiza da zuciyarsa tayi. Cikin bayyanarda tsananin tashin hankalinsa yace, Zata aikata wani babban kuskuren sbd rusa karagar gabaki 'daya na nufin rusa rayuwarta sbd zata rushene tareda jininsu jamal na qarshe daya hau karagar yayi mulki akanta...... Shiru yayi zufa na karyo masa sbd yasan dagashi sai itane suka rage aduniya wainda suka taba zauna karagar har sukai mulki akanta, A bangaren jini kuwa shikadaine jininsu na qarshe dayayi mulki akan mineelik ita 'din ba jininsu bace akwai yiyuwar abin bazai shafetaba koya shafeta saidai ta nakasta amma shi babu tantama rayuwarsace ke rawa jinin qarshe nasu jamal. Wannan rumanah gabaki 'daya rayuwarta ta zame masa masifa mai barazana bai taba tunanin ko namiji zai iya fuskantarsaba ya girgizasa bare 'yaya mata daya dauka marasa amfani saigashi ko acikin 'yaya matan ma baiwace take barazaga rayuwarsa, Bazai Bari su aikata hakanba dole ya juya musu zancen.. Gyara nutsuwarsa yayi cikin vasarwa yace, Karku bari ta aikata hakan sbd rayuwartace acikin hadari dan kuwa haqqine na qarshe zai fita akanta..... Murmushin baqin ciki ammy tasaki tareda girgiza kai hawayenta suka sauko tace, Yanayinka da kulawar daka nuna yasamin kokwanto akan amsarka dan haka mun dangana munbarwa Allah komai zamu barta takawo qarshen mineelik duk abinda Allah ya qaddaro zamu runguma mu dauki dangana. Miqewa tsaye tayi zata fice ya riqo hannunta akaro na farko dayaji tsoro da fargaba sun ziyarci zuciyarsa ya bude baki daqyar yace, Karki bari ta aikata sbd rayuwatace a hadari kuma tatama na cikin hadari. Hawayenta suka qara gudu ta sunkuyar dakai tanajin zuciyarta na karyewa sbd qaunar mijinta uban yayanta saidai kuma kodan sbd 'yayanta da jikokinta zataso akawo qarshen masifar mineelik. Zame hannunta tayi ahankali tace, Allah yazaba mana abinda yafi zama alkhairi. Ficewa tayi jiki asanyaye zuciyarta na sake karyewa saidai bazata bari ta karayaba hakan da rumanah zatayi shine daidai insha Allah. Zaune yake bakin gadonsa yayi shiru tareda zurfi cikin tunani Sam bayajin nutsuwa a zuciyarsa wani irin rashin sukuni yakeji.. Ahankali tashigo dakin rungume da abeel jikinta amatuqar sanyaye sbd jikinta datake yana tsananta dan ko yanxu kafin tafito saidata yanke jiki ta fadi jini na fita hancinta saidai bata fita hayyacinta ba kuma ta hani Jakadiya fadawa kowa abin yafara tsanani. Qarasowa tayi ahankali ta kwantarda abeel kan sofa tadawo gefensa ta zauna ahankali tareda dafa hannunsa takalli fuskarsa. Shima ita ya kalla ta sakar masa murmushi ahankali tareda riqe hannunsa ta lumshe ido sbd abinda taji yana taso mata ta danne yanayin daqyar tasake qaqalo murmushi tana kallon hannunsa dake cikin nata ahankali tabude baki tace, Karka saki hannuna har lokacinda zan shaqi numfashin qarshena a duniya, Ka zamo jiqo kuma majingini arayuwata Ka hanani 'daukar hanyarda zata batardani zuwa duniyar daba tawaba, Qarfin soyyarka yaci qarfin abinda nakeji ajikina saidai bansaniba ko hakan zai jima shiyasa a yanxu nake roqonka da har abada karka rabu da suhailat sbd itace macen da soyayyarta bazata taba barin cuta ta kutso kai rayuwarkaba..ni tamkar baquwace a rayuwarku ba lallaine na qarasa rayuwa acikinkuba....... Matse hannunta dake cikin nasa yayi yana rintse idanuwansa dasukai jajir.. Hawayen datake riqewane suka 6alle mata ta kalli fuskarsa datai jajir ya rintse idanuwansa ta shafi fuskarsa hawayenta na tsananta tace, Maheer abdulshams nagode da soyayyarka gareni.. Bude jajayen idanuwansa yayi yana kallon hawayenta dake gudu sosai yakasa magana sbd radadi da nauyin da zuciyarsa tai masa sai kawai ya rungumota jikinsa. Ahaka suka kwana cikin wani irin sanyin jiki dana zuciya. Kwanansu khaleefa biyu a ruwa aranar na uku da yamma sosai suka isa saidai kuma sunsha wahala sosai sbd tuni bakin ruwan yazama border saida sukasha wata irin wuya kafin suka samu wucewa da taimakon wani 'dan asalin qauyensu mamani din. Bayan wucewarsu duk yanda sukayiwa saurayin bayani bai ganeba sbd basajin hausa ko kadan har gwara nuratu tanaji kadan kadan sbd su mamani da umman rumanah sunayi musu tun suna qanana saidai ya jasu kan mashin dinsa sukayi wani irin mugun overload yajasu dan kaisu cikin qauyen daya samu canji ba laifi. Tafiya mai tsawo sukayi kafin suka isa qauyen mai tsananin girma da cikar mutane. Gidan shugaban qauyen yakaisu cikin sa'a lokacinda suka isa yana gida. Kallonsu aka taru anayi sbd ganin baqaqen labarawa musamman khaleefa dayake cikakken dan Ethiopian asali. Bayan anbasu guri sun zauna ya fidda tambarin masarautar dasuka fito ya miqawa shugaban ya kalli nuratu yayi mata magana yace, Kiyi musu bayaninmu yanda zasu gane ko yayane. Gyara zama tayi muryarta na rawa tace, Munfito daga qasar Ethiopia ne qarqashin masarautarsu, Sun siya bayin dasuka fito daga wannan nahiyar tsawon shekara ashirin da biyar yanxu., Acikinsu akwai mamani da asma'u dasuka tafi da juna biyu acan suka haifi 'yaya mata dukkaninsu Wanda 'daya daga cikin 'yayan itace ni 'dayar kuma a yanxu itace sarauniyar qasar. Da wani irin mugun mamaki suke kallonta musamman shugaban garin daya zamto kutti mijin mamani yasake kallon nuratu da gabaki 'daya take kamar yar asalin Ethiopia itama. Cikin nutsuwa yace, Ke 'yar wacece acikinsu? Ni 'yar mamani ce. Wata irin kabbara tsoffin gurin suka dauka cikeda murna da mamakin wannan alamari kutti yace, Ina iyayenku? Dukkaninsu Allah yayi musu rasuwa mamani ko sati batayiba yanxu haka. Sake daukar kabbara sukayi cikin jimami da tsananin girmama wannan alamari. Ahankali ta zayyane musu komai gameda rayuwarsu kafin ta gabatarda khaleefa amatsayin Wanda zai karbi takardun dukiyar asma'u da bulama dan neman asalin sarauniya ummu-rumanah. Bayan dogon koke koken saduwa da baqin cikin rashinsu mamani dasu bulama nan kutti yagabatarwa da su nuratu kansa amatsayin mahaifinta. Duk wani zuriar gidan antaru an karbi nuratu da hannu Bibbiyu da zuciya daya da wainda suka San faruwar abin da wainda ma ko haihuwarsu baayiba nan dai kowa yataru ana farin ciki. Ganin yanayin garin yasa khaleefa yanke shawarar wucewa dan sake kutsawa cikin Nigeria dan gabatarda abinda yakawosa. Kutti ya basa takardun dasuka tsufa sosai ga sanyin ruwa daya soma lalatasu tun wancan lokacin saidai ba laifi yana iya ganin rubutun dake jikinsu atake ya karancesu daganan ya roqi alfarmar tafiya da wani yaron kuttin dayake jin yarensu kadan kadan sbd aiki dayakeyi a border dinsu. Da mashin din salee suka isa inda zasu samu mota bayan sunyi tafiyar awowi akan mashin din. Motar dazata kaisu Maiduguri kai tsaye suka hau inda duk hankalin khaleefa yatashi sbd ganin inda yasamu kansa dakuma wata irin azabar wuyar tafiya data fara gigitasa. Gaf da asuba suka isa Maiduguri kai tsaye wani lafiyayyan babban hotel suka sauka anan yayi baccin wahala ga zazzabin dakeson kamasa na baqar wuyar dabai taba shaba. #mamuhgee [8/7, 7:37 AM] ummul aulad: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *45* Not edited. Saki jikinsa yayi sbd wutar data daukewa jikinsa da wani irin qarfi ammy ta jijjigasa tareda kiran sunanda da qarfi ya durqusa tareda jawota jikinsa ya dauketa gabaki 'daya yabar gurin da ita. Anso tsayarda nadin sarautar amma haroun ya fitarda saqonta na gaba dake cewa duk abinda zai faru kar a tsayarda nadin dakuma takardarta tagaba dake cewa a raba mara masarautar biyu a rushe Rabin a gina masallacinda yafi kowane girma a qasar Ethiopia. Hakan yasa aka cigaba da nadin yayinda sultan dake zaune har aka gama bai motsa daga inda yakeba saida aka watse aka gano ya rasu zaune agurin gakuma jinin da aka ganin ya digo daga hancinsa. Lokacinda su negasi suka rufu akanta dan ceto rayuwarta alokacin ne aka zo da saqon rasuwar sultan Wanda ya girgizasu ya qarasa wargaza dukkanin sauran nutsuwarsu musamman ammy data kasa riqe kukanta maheer yayi saurin rungumeta yana riqe nasa hawayen sbd Allah yasani yana qaunar mahaifinsa duk mugun halinsa sbd koyaya ya zama mahaifinsane. Cikin qanqanin lokaci rasuwar sultan da halinda assultana take ciki tareda canza karagar mineelik suka yadu 'yan jaridu da kafafen yanda labarai sukaiwa masarautar wani irin dandazo ana yada abinda ke faruwa. Dukkanin iyalan marigayi abdulshams sun halarto cikin tsananin baqin cikin wannan rana data riskesu musamman 'yayan marigayiya adama dasuke ganin sun rasa uwa da uba. Da maraice akai jana'izarsa inda dubban alumma na nesa dana kusa suka hallara inda yawan jama'arsa yasa maheer jin sanyi sanyi aransa tareda yiwa mahaifinsa adduar samun rahamar Ubangiji. Duk damuwar dayake ciki ta halinda rumanah take ciki bai koma gurinta ba sai dare bayan an watse. Kai tsaye sashen ammynsa ya nufa inda ya tararda ita tareda sauran 'yan uwansa ya qarasa kusada ammyn ya zauna yana kallonta cikin nutsuwa da tausayawa ya riqo hannunta ahankali ya iya furta, Allah yaji qansa ammynah. Kwantarda kanta tayi kafadarsa tareda cewa "amin" da muryarta data shaqe kafin ta 'dora da fadin, Kaje gurin rumanah dan sanin halinda take ciki duk da meenah da jakadiya na gurinta. Jinjina kai yayi jikinsa na qara sanyi da tuno wani tashin hankalin dayake ciki. Lokacinda ya isa sashenta har lokacin bata farfado ba sai jinin daya tsaya Wanda suke sakaran jinintane yayi matuqar qasa sosai. Zaune ya kwana gabanta yana mata addua cikin wani irin hali dabai ta6a tsintar kansa aciki ba. Washe gari koda akaga bata farkaba hankula sukai matuqar tashi musamman da jikinta yayi wani irin fari fari Kore Kore ga 'yan jarida dasuka kasa suka tsare a masarautar sunason ganawa da sarauniyar data kafa sabon tarihi a qasar daba tataba. Duk wani kalar likiti na turai da gargajiya an nuna qwarewa amma abu yaci tura gashi alamunta na sake 6aci ranar da akai uku aranar gabaki dayansu suka tattara suka nufi Georgia..shi,ammy da jakadiya data samu 'yancin rayuwarta itama sai sauran 'ya'yan da kowace takoma inda take aka bar sabon sultan dan gabatarda mulkinsa cikin aminci. Suna sauka kai tsaye motar asibiti tazo daukarsu aka wuce asibiti dasu cikin tashin hankalinda yafi na farko sbd saki jikinta daya farayi. Matsayinsa a babbar asibitin garin yasa ana isa da ita dukkanin likitocin dake nan suka taru aka fara qoqarin gano matsalar cikin gaggawa cikin tashin hankali da mamakin yanayin matsalarta sbd basu taba cin karo da irin hakanba. Ammy daqyar ta iya zama gida saidai gabaki 'daya hankalinta da damuwarta na asibitin gabaki daya cikin kwana ukun ta rame tayi wani irin sanyi ko doguwar magana bata iyawa. Har gari ya waye likitoci na kanta duk wata dabararsu da qwarewarsu sun nuna dan ganin ta farfado saidai Sam bata farfado ba saidai fatarta data fara komawa daidai sbd jinin da aka saka mata kusan leda biyu hakan yasa suke sakaran idan fatar ta gama komawa daidai ta farka. Daqyar yake iya hadiye yawun bakinsa sbd tsananin bushewar bakinsa da maqoshinsa, Duk wata nutsuwarsa da tunaninsa sungama barin jikinsa idanuwansa tuni suka qanqance ko gani bayayi sosai da idonsa dukkanin abokanan aikinsa sun tausayawa halinda yake ciki shiyasa suma gabaki daya hankalinsu tashe yake da ganin ta farfado 'din. Khaleefa aranarda suka wuce aranar yasauka Ethiopia ya tararda abinda ke faruwa kasa kwana yayi duk da rashin lafiyarsa washe gari yabi jirgin asuba sbd yasan aminin nasa na tsananin buqatarsa. Har yamma bata farkaba khaleefa ma saukarsa garin alhaji babaye yakirasa sbd news din dasuka gani gameda abinda yake faruwa a qasar nan yaqara yasanardasu abinda yake faruwa nan hankalinsu yayi matuqar tashi suka fara shirye shiryen tahowa cikin gaggawa. Qarfe goma na dare ta bude idanuwanta dasukai wani irin shigewa sukai nauyi da ja. Atake dukkanin likitoci suka sake hawa kanta cikin gaggawa da nuna qwarewa tareda fatar samun nasarar sanin matsalarta. Kasa miqewa yayi sbd saki ga gabobin jikinsa sukayi sbd fargabar abinda za'a fada masa saidai khaleefa ne ya dafasa yana jinjina masa kai alamar qwarin gwiwa ganin halinda yake ciki. Wasu sabbin dogayen hours suka 'diba suna qoqarin gano matsalar wadda suka gano daga qarshe wadda tayi mummunan 'daga hankalinsu haka suka ringa fitowa jiki amatuqar mace zuciyoyinsu ba dadi sbd dukkanin hotunansu da test test dinsu sun tabbatar musu da abu 'daya. Dr Edward ne yafito qarshe yana zare glasses dinsa yakalli maheer da khaleefa yace, Can we talk in my office pls.. Tashi tsaye maheer yayi tareda kallon qofar dakin da take yakalli Dr Edward din yana rintse idanuwansa da abinda za'a fada masa yace, Just tell me dr Edward I c........ Dafasa Dr Edward yayi cikin tsananin tausayi ganin daqyar yake iya bude bakinsa yayi magana cikin sanyin murya yace, I'm really sorry Dr m.a shams matarka ta rasa gangar jikinta bazata taba gara aikiba ma'ana tanada rai tana gani tana numfashi tanaji saidai bazata iya motsa jikintaba ko kadan bare magana har abada. Wani mugun jirine ya dibesa khaleefa da Dr Edward sukai saurin nufarsa zasu taresa ta rigasu taresa cikin kulawa da tausayawa. Khaleefa ne yakalleta cikin mamaki Dr Edward kuwa jinjina mata kai yayi alamar ta kula da maheer din yana buqatarta fiyeda koyaushe. Shikuwa idanuwansa na ganinta baisan sanda ya sake fadawa jikinta yana qoqarin tsaida hawayensa saidai Sam basu tsaiduba saida suka zubo ya sake qanqameta yana cewa, Suhailat please pray for me wlh zuciyata zafi takeyi I just can't live without her sbd wannan ma baida banbanci da mutuwa agareta. Murmushin tausayinsa tasaki cikin sanyin murya tace, Insha Allah zata warke Nayi maka alqawarin zamowa majingini agareka duk lokacinda kake buqatata wannan alqawarin yananan haryanxu kuma nayi alqawarin cika makashi har qarshen rayuwata kuma zan tayaka jinyarta harta ji sauki sbd sonka shine qaddarata maheer abdulshams.. 'Dagowa yayi kalleta da idanuwansa itama hawayen takeyi tana murmushi ahankali yaji wata irin soyayyarta mai tsafta tashiga zuciyarsa akaro na farko cikin wata irin rawar murya yace, I love you suhailat sbd kece hasken rayuwata dakike tallafoni koyaushe. Wasu hawayene suka gangaro mata ta rintse ido tana kwabar zuciyarta dake neman shegala da kamansa datasan ta samesune sbd nuna qaunarta ga rumanah saidai matuqar qaunarta ga rumanah zata jawo masa soyayyar mijinta to tabbas ta shirya samun soyayyar mijinta ta hakan. Duk yanda ya 'daga hankalin likitocin asibitin akan abinda sukace dole ya dangana yadauki qaddara sbd result din dayane. Ko ammy saidata kwana ta yini tana kukan halinda rumanar ke ciki da Wanda yashiga sbd gabaki daya ya birkice musu ko abinci sai ammyn tayi kuka yake iya shan abu mai ruwa ga suhailat data zamo batada wata hidima saita kula da dukkaninsu sbd sundawo gida. Idan yazo ya zauna kusada ita haka zai riqe hannunta cikin nasa ya qura mata ido Itadai hawayene kawai ke iya gangarowa ta gefen idonta musamman idan ammy tasata gaba tana kuka kokuma shi idan yazo ya zauna yasaka gaba ya qura mata ido tana iya hango mawuyacin halinda yake ciki. Ranarda su hajiya yakurah suka iso aranar kuka yadawo sabo ganin halinda 'yarsu dasuke 'dokin gani take ciki... Ko alhaji babaye dake dattijo saida ya zubarda hawayen baqin ciki da farin ciki. Akwance take itama amma hawayene keta bin gefen fuskarta suna zuba Wanda hakan yaqara bawa kowa tausayi. Duk da akwai Carolina sosai suhailat ke wahala sbd lalurar rumanah din. Kusan satinsu alhaji babaye biyu kafin shi ya koma yabar haj yakurah dataqi dawowa tana jiran isowar mijinta dazasu tafi tareda rumanah sbd gwada nasu na addinin. Satin alhaji babaye daya da tafiya alhaji mukhtar mijin haj yakurah ya iso kallo 'daya yayi mata yagano lalurarta Allah takeson akomawa sbd lalurace ta iska nan take suka yanke shawarar tafiya da ita maheer kai tsaye ya nuna rashin amincewarsa Saidai ammy dataga yana mutuwar tsaye kullum sbd lalacewa da rayuwarsa ke nemanyi dan ko aiki bai taba fitaba koyaushe yana gida ga suhailat data zamto abar tausayi gurin qoqarin kulawa dashi da rumanah duk ta rame tausayinta da qaunarta yasa kai tsaye ta zaunar dashi cikin nutsuwa ta fahimtar dashi kuskuren dayake jefa rayuwarsa da iyalinsa ciki dan haka yabar rumanah aje da ita ya tsaya ya gyara mu'amalarsa da rayuwar aurensa da suhailat. Sosai jikinsa yayi sanyi kuma yasan matuqar yanason gyara rayuwar iyalansa ta inganta saiya boye soyayyar rumanah kwata kwata dan haka zai danne Zuciyarsa yafara daga yanzu. Da haka ya amince aka tafida rumanah din amma hardashi suka tafi saidaya kwana biyu yadawo dan qoqarta gyara mu'amalarsa da suhailat. Koda yadawo su ammy da jakadiya tareda abeel sun komawarsu Libya dan haka gidan dagashi sai suhailat sbd su amah ma suna Mali tabarosu dama itakadai tazo. Aranar daya dawo lafiyayyan tarba tayi masa cikeda Dari darin yanda zai dawo yayi rayuwa a inda babu rumanah. Ganin yanda take kama kanta dashi duk sai yaji ya muzanta ya tattaro jarumtarsa ya danne abinda ke ransa ya riqo hannunta ahankali tareda jawota jikinsa yana kallon fuskarta dake kallonsa yasaki qayataccen murmushi yajata suka zauna bakin gadon dakinta daya shigo yasameta hartayi shirin bacci zata kwanta. Kallonsa takeyi tanason gano damuwarsa saidai takasa ganin komai sai murmushin dayake sakar mata Wani irin sanyi da farin ciki taji na shigarta ahankali kenan kalamansa daga zuciyarsa suka fito lokacinda yafada matasu. Rungumesa tayi da sauri tana sakin hawayen farin ciki ta murmushin jin dadi. Dagota yayi tareda zare mata riga yana murmushi yace, Banyi wankaba so yau kece zakiyi wannan aiki. Noqewa taso yi tana murmushi yayi saurin riqeta yana kallon cikin idonta ya girgiza mata kai ahankali yace, Don't make that mistake again suhailat. Kallonsa tayi tareda jinjina kai takama hannunsa ta nufi hanyar toilet dinta dashi suka shige. Aranar wata irin rayuwa suka gudanar data mantarda suhailat dukkanin damuwarta ta dah inda sukai alqawarin dora sabuwar rayuwar aure ta fahimta,soyayya qauna da aminci atsakanin su uku da 'yayansu daga yanxu. ** Ahankali ake gudanar da adduoi da sauran abubuwan addini tareda sauke al-qur'ani da sadaka ana fatar samun sauqi. Kulawa sosai da wata irin qauna da soyayya suke mata kaf zuriar banda zuriar gidansu aqeel data gama tarwatsewa babu wani nakamawa acikin zuriar gidansu shiyasa koda sukaji 'yarsu bulama tadawo kuma a nakashe kota kan zancen basubiba. Su kuwa haj yakurah tamkar 'yar data haifa da cikin ta takejin rumanah duk wata kulawarta da dukkanin hidimarta takoma ta rumanah shima alhaji babaye kullum saiyazo gidan sbd yayi yayi tabari rumanah takoma gidansa taqi yarda tabari. Watanta hudu a Nigeria yazo dubata babu adadi duk tareda suhailat suke zuwa Wanda itama tanajin farin cikin ganinsa da suhailat sbd ganin hankalinsa ya 'dan kwanta sosai duk sukazo idan zasu tafi daurewa kawai yakeyi yakoma sbd alqawarin adalci daya daukarwa kansa. Ammy kuwa kusan tamafi maheer din zuwa kuma takan dade idan tazo. Ahankali tafara samun sauqi sbd wasu gurare dasuka fara motsawa ajikinta Wanda hakan ba qaramin farin ciki da qwarin gwiwa yasakasuba nan aka sake maida himma ga sauke al-qur'anai da sadaka da adduoi. Ba'a rufa wata biyu da fara motsinta ba tafara magana ahankali har tana iya tashi zaune da kanta ta tashi. Lokacinda wannan saqon ya iso masa aranar suhailat harda hawayen farin cikin ganinsa cikin tsananin farin ciki mara misaltuwa tayi sbd Sam kasa boye farin cikinsa yayi. Kafin sati biyu dukkanin kuzarinta sun dawo lafiya kalau saidai bata iya komai da sauri ko qarfi Wanda hakan shima ahankali zai dawo. Washe garin ranarda umma yakurah da ammy suka fada masa samun lafiyarta yatafi wannan karon suhailat qin biyosa tayi sbd ganinta kusa zai hanasu nuna kewar junansu. Sai dare sosai ya isa Wanda tareda khaleefa dazaije gurin nuratu sukayo tafiyar dole suka sauka masaukinsu kai tsaye sai washe gari suka nufi gidan guraren qarfe goma shima sbd khaleefa daya hanasu tafiya tunda safe. A babban palo suka tararda su umma da ammy harmada Jakadiya da sabuwar mai rainon abeel suna ganinsa umma tayi murmushi sbd tanajin dadi da farin cikin yanda yake tsananin qaunar rumanah dinsu. Ammy ma dariyar tayi masa inda aka gabatar musu da abincin breakfast saidai sunyi breakfast already. Duk yanda yaso ganinta qin barin su kebe umma tayi qarshema anan palo tasa Nana aishat 'yar autarta taje kairawo rumanah din tajima kafin yafito sanyeda dogon hijabi har qasa daya matuqar yimata kyau sbd wannan ne karo na farko daya ganta sanye dashi itama anan din takoya sakashi sai tanajin dadinsa. Kasa 'dauke mayun idanuwansa akanta yayi musamman yanda ta canza sosai takoma kamar ba rumanarsaba datasha wahalar rayuwa dan lokacin. Wani irin murmushi yasaki Wanda shikadai yasan yayi abinsa sai ita data gani ta dauke kai tana gaidasu cikin yarensu sbd har gwara khaleefa yafara son koyar yaran Hausa sbd nuratu dayake yawan ziyarta shikuwa haryanxu yakasa koyan komai. Koyaushe da turanci yake magana dasu umma da alhaji babaye hakama ammy. Kwanakinsa uku amma Sam umma taqi barinsu kebewa hakan ya matuqar dama lissafinsa shiyasashi tattarawa yakoma gashi ko waya basayi bare yarage zafi. Koda yadawo suhailat ta lurada bai cikin dadin rai da walwala saidai batai shishigin tambayaba tunda bai shiga haqqintaba. Bayan sati biyu kai tsaye yakira alhaji babaye yasanardashi yanason rumanah tadawo tunda taji sauqi koda alhaji babayen yayiwa umma magana kai tsaye tace sai wani wata sbd zasuyi walima dakuma 'yan shirye shirye. Baisoba amma sbd ammy data basa hakuri saiya bari din badan yasoba. Hidima sosai da gyara irin nasu na asalin 'yan Maiduguri. Taron biki sosai akayi tamkar yanxune zaa daura mata aure akai walima da yinin biki na alfarma inda ko nanma 'yan jarida basuyi qasa da gwiwaba sunxo ganawa da tsohuwar sarauniyar qasar Ethiopia saidai maheer daya bada gargadi mai qarfi akan karta kuskura barin kowa yadauki hotonta ko fira da ita. Lokacinda nuratu ta iso gurin bikin sosai sukayi farin cikin ganin juna dakuma auren nuratun da khaleefa keson yi. Irin gyaran da akai mata da shirin da akai mata ita kanta burge kanta takeyi ga wani irin qamshi daya kama jikinta. Dukiyarta kai tsaye tace suci gaba da kulawa da ita tabar musu halak malak bata buqatar komai. Ranarda zasu tafi ammy ce da jakadiya sai umman da matar alhaji babaye da yaransu 'yan mata da nuratu suka rakasu har Libya tareda dukiyar aure mai tarin yawa inda sukai kwana biyu suka juyo suka barota. Sabuwar rayuwa ta bude a Libya inda nanma ammy wani gyaran ta dora ranarda tacika kwana shida cif aranar aka sai mata ticket ta wuce batareda abeel ba. Qarfe uku na yamma jirginta ya sauka suhailat ce tazo daukarta sbd ogan na hospital gurin aiki baimasan aranar zata dawoba ammy suhailat kawai tafadawa shiyasa tazo daukarta. Cikeda farin cikin ganin juna suka rungume juna suhailat na mata sannu da zuwa da cewa, Where is my abeel? cikin farin ciki ta amsa tana cewa, Ammy ce ba ruwana. Wani gida na daban taga sun nufa Wanda yafi nada girma sosai tun a harabar gidan ta fahimci kowaccensu nada wadataccen gurinta yanxu. Da gudu su amah suka fito suna mata oyoyo ta riqe hannun fammah data fara mantata tayi kissing goshinta tana cewa, Famman mum 'dinta. Babban lafiyayyan qaton palonsu suka shiga nan suhailat ta rakata da luggage dinta har cikin dakinta dake daukeda parlour da two bedrooms aciki ga komai nata is white. Bayan fitarsu wanka tashiga tana fitowa tayi sallolin dake kanta dasu magrib da akayi tana gamawa ta shirya cikin pencil skinny jean blue daya kama cinyoyinta da White shapeless top sai White club scarf data rufe kanta dashi ta fito fiddo wayarta daga handbag dinta taga misscalls dinsu umma da ammy harma dana nuratu tafara kiransu daya bayan daya tana cikin wayane da ammy suhailat tashigo tana murmushi itama cikin adonta na wani black straight skirt daya fiddota da red chiffon top gashinta daure saidai bata saka hula ba tace, kiyi sallar ishai kifito muyi dinner already your ango is home. Murmushi tayi tana cewa, Ok ganinan zuwa. Sallar ishai tayi tana gamawa ta gyara scarf dinta tareda fesa turare da humra mai sanyin qamshi ta fesa mouth freshner abakinta ta dauki wayarta ta fito. Zaune yake kan dining din shidasu amah sai suhailat dake qoqarin zama ta gama zuba nata abincin Ta bayansa yajiyo wani irin qamshi ya lumshe ido ya bude dan tabbas kodata canza turare kusancinta sanannene a zuciyarsa tana qarasowa gabansa abincin daya saka bakinsa ya sarqesa ya rufe baki yana tari da sauri suhailat tabashi ruwa tana dariya tace, Easy karka illatamin kanka she's really here ba gixo bane. Karba yayi yasha yana watsa mata wani kallo yace, Dake aka hada baki right... Murmushi tayi tace, Ba ruwana ammy ce. Juyowa yayi ya kalli inda take cikin wani irin shauqi da tsananin soyayyarta dake fizgar zuciyarsa duk yunwar dayakeji ta bace. Ita kuwa abincinta takeci hankali kwance duk da zuciyarta rawa takeyi sbd irin kallonsa datakeji yana yawo ajikinta. Barin dining din yayi sbd zai iya bada kansa yakoma kan kujerun palon ya zauna yana canxa channel zuwa news duk da dai Sam baimasan meyakeyiba sbd halinda zuciyarsa take ciki. Bayan sungama Carolina ta tattara gurin suhailat takaisu amah daki sukai duk abinda zasuyi suka kwanta saidata tabbatarda sunyi bacci tafito lokacin ba kowa palon kowa na dakinsa. Dakin rumanah ta nufa kai tsaye tayi mata saida safe tareda sanarda ita kwana biyu biyu zasu riqa yi tace mata tou. Tana sane ta sharesa taqi zuwa gurinsa ta tube ta dauko rigar baccinta zata saka saidata daga hannuwanta zata saka taji an zare towel 'dinta da sauri ta juyo Ashe amatse yake da ita tana juyowa sai a jikinsa atare suka sauke ajiyar zuciya yana zare rigar hannunta yayi jifa yana kallon cikin idanuwanta dashi itama take kallo. Jikin wardrobe ya matseta yana cigaba da kallonta zuciyarsa cikeda wani irin farin ciki ahankali yace, Wani irin sone zuciyata ke miki ummu-rumanah bulama. Kunnensa takai bakinta cikin wani irin salo tace, Irin sonda ummu-rumanah kewa maheer abdulshams.. Wani irin murmushi yasaki tareda hade fuskarsu sbd tsikar jikinsa data tayar masa ya dora bakinsa kan nata yace, I love you ummu-rumanah bulama. I love you more maheer abdulshams. Hade bakinsu yayi suka saki numfashi atare cikin tsananin kewar junansu ya cirata suka isa gadonta ya zura hannu ya kashe wuta. Washe gari da wuri ya tashi yayi shirin office bayan sun gama lalacewarsu har gurin wanka. Atare dukkaninsu sukayi breakfast kafin shiya fara fita tukuna yaran sai suhailat data futa qarshe. Yaso dawowa gida da wuri amma sbd dorarta zaman lafiya da qauna tsakanin iyalinsa yafasa harsaida lokaci yayi yadawo. A ranarma a dakinta suka bajewarsu saidai duk yanda yaso qin latti saidayayi sosai. Watanta shida da dawowa tafara laulayin ciki Wanda take samun kulawa sosai daga garesu har Allah yasauketa lafiya tasamu 'yan biyu mace da namiji. Zaman lafiya kwanciyar hankali tareda aminci da qaunar juna mai cikeda fahimta suke gudanarwa tareda girmama juna. *_ALHMDLLH nan nakawo qarshen tarayya da yardar Allah masoya ina miqa godia sosai sbd wlh yawanku bazai bari na iya batokuba._* *_Kusani dai mamuh takuce kuma natane._* _*idan nayi kuskure kokuma mantuwa ta Kumin uzuri yanayi rubutune Allah yabamu ikon daukar darasin ciki.*_ *_FAHIMTARWA..._* *_Idan marubuci yayi rubutu za'ace bai San abu ba baiyi bincike akan abu ba amma yaje yarubuta sbd shirme da rashin sanin meye rubutu.._* *_Tou kuma idan mutum yayi binciken yarubuta yanda abin yazo ace baida ilimi.._* *_Labarin tarayya yaxone akan tun asalinsu ba musulmai bane akwai kafurci jahilci ataredasu Wanda hakan duk shine silar komai dan haka dole sai an bayyanarda jahilcinsu da kafircinsu ta hanyar sunayensu da ayyukansu yanda labari zai tafi daidai.....ga masu cewa sunayen ciki basu halastaba kenan..._* *_Masu cewa babu addini,babu riqo da addua da basu komawa Allah ba kuma ta yaya zasuyi hakan bayan anbayyanar dasu marasa sani acikin labarin idan lokacin yi da amfani da hakan yakai ai za'a sakane..._* *_dan Allah muriqa duba asalin tsarinda aka 'doro labari mu riqa binsa daki daki dan sanin abinda zamu riqa cewa._* *_Nagode Allah yaqara sadamu gaba._* [8/7, 7:38 AM] ummul aulad: *_TARAYYA_* _wattpad@mamuhgee_ _Haske writers association💡_ *44* Not edited. Duk yanda yaso yayi komai cikin lokaci yakoma hakan bai samuba sbd zazzabi mai qarfi daya kwantar dashi tsawon kwana biyu Qarshe dai dole ya daure suka tafi kai tsaye companyn dake rubuce a jikin takardun da taimakon wani ma'aikacin hotel din suka isa. Da farko sunsha wahala kafin suka samu ganin shugaban companyn alhaji babaye salmanu bulama. Kai tsaye khaleefa yafitarda takardun dayazo dasu ya ajiye gaban alhaji babaye. Kallo daya yayi musu harzai dauke kai yayi magana yaga sunan dake jikinsu yayi musu wata irin damqa yana dubawa sbd basuyi masa kama dana yanxuba wannan rubutu da sunan company dinne tunna iyayensu na shekarun dasuka wuce. Budesu yaringayi daya bayan daya haryakai qarshe ya miqe tsaye sbd tabbarda sune asalin takardun da 'yayansa da matarsa suka tafi dasu. Kallon khaleefa yayi da sauri tareda zagayowa daga table dinsa jikinsa na wata irin rawa tun kafin yayi magana khaleefa yaciro alamar masarautar daya fito ya miqa masa cikin turanci yace, Nazone dan neman asalin sarauniyar qasata ummu-rumanah bulama.. Rawa jikin alhaji babaye yaqara yace, Ina kasamo wainnan takardun? Ina masu su suke? Masu wainnan takardun sun rasu saidai 'yarsu wadda itace sarauniyar qasarmu ayanxu.... Wani irin kuka alhaji babaye yasaki tareda rungume khaleefa duk da dai yasan dole yayi bincike akan hakan kafin yagama yarda. Waya yaciro yakira qanwarsu  hajiya yakurah yafada mata nan hankali ya tashi sbd farin ciki da murna tareda wasi wasin zamtowar zancen gskia. Da kansa yakaisu gidansa akai musu masauki kafin yatabbarda zancen duk da yasan baza'a yimusu qarya dan a cucesu tun daga qasar Ethiopia ba kuma daga masarautarsu. Washe gari cikin manyan motoci suka dunguma zuwa garinsu kutti dan sake tabbatarwa. Sai tsakiyar dare suka isa kuma acikin daren aka tara duk dattijan garin dasukasan su bulama da asma'u tun zuwansu garin da duk abinda yafaru. Kuka sosai alhaji babaye yayi dayaji irin rayuwar da 'dan uwansa da matarsa sukayi saidai kuma yanzu babu abinda yakeson gani kamar 'yar dan uwansa. Daga alhaji babaye sai khaleefa suka koma sbd khaleefa jirgi zaibi yakoma bazai iya tafiyar ruwaba kuma sauran binciken da tabbatarwar idan sun haduda rumanah zasu qarasa tabbatarwa. Koda suka koma gida sosai hajiya yakurah taso bin khaleefa suje tare saidai maigidanta yace tabari yadawo daga China saisuje gabaki dayansu da haka khaleefa yatafi sbd ciwo dake neman kwantar dashi sbd bai qaramar wahalaba yasha a tafiyar. A yau saqon haroun ya iso gareta an kammala aikinta. Shiru tayi bayan fitar Jakadiya sbd tunanin yaya maheer zai karbi zancen sbd dole tana buqatar aiwatarda abinda tayi niya dan tanaji jikinta yasaki sosai jininta qarewa yakeyi sbd tsananta da abin yafarayi ajikinta sbd jinin dataqi zubarwa har lokacin tasan daf take da rasa hankalinta dan wata irin zabura dake kamata yanzu duk da tana qoqarin boyewa ammy da maheer tanaji abin yafara cin qarfinta. Kallon abeel dake kwance jikinta tayi zatai magana jini ya digo ta hancinta ya sauka kan fuskarsa tayi saurin goge masa tareda ajiyesa ta dauki tissue tana dafe kanta da jiri ke juyawa dashi. Durqusa gurin tayi tana fidda wani irin nishi cikin azaba tsawon mintuna kafin tasamu taci qarfin abin tana kiran sunayen Allah harya lafa kafin tayi wani yunqurin miqewa ya turo qofar dakin yashigo cikin nutsuwa idanuwansa kanta yana kallon tissues din gabanta dasuke lalace da jini hakama hancinta zuwa bakinta duk jini. Saurin goge hancinta tahau yi saidai kuma atake jinin yasake 6allewa ta rintse ido cikin wani irin hali tafara nishi mai wuyar fita. Da wani irin gudu ya qaraso gareta tun kafi yakai hannunsa gareta idanuwanta suka fara qoqarin rufewa yayi saurin tarota jikinsa yana kiran sunanta da qarfi. Ganin tana neman fita hayyacinta yasa ya bude bedside drawer dinta yadauko maganin da negasi yabayar ariqa bata idan jinin yazo mata ya bude gabaki daya ya zuba mata abaki cikin tashin hankalin saidai jinin bai tsayaba amma idanuwanta sun bude tafara qoqarin tashi tana karbar tissue din dayake qoqarin kaiwa hancinta tace, Banda lokaci inason sanardakai abinda nake ashirin aikatawa ayau sbd banason na mutu abanza batareda na tsayarda abinda ke faruwaba..... Wani irin tari tayi jini mai tarin yawa ya fito bakinta kamar amai Atake ya rungumota abinda bai taba ba arayuwarsa hawaye suka gangaro masa yafara girgiza kai yana hanata magana.. Girgiza masa kai tayi awahalce tace, Taimakeni na shirya muje mukawa qarshen matsalar sbd 'yan baya su samu nutsuwa da kwanciyar hankalin gudanarda mulkin adalci. Kasa motsi yayi saidata saki kuka ahankali tana kallonsa cikin rawar murya tace, Karka manta ka min alqawarin tsayawa dani dan kawarda matsalar data lalata farin cikinmu dana wainda basujiba basu ganiba. Cikin wani irin hali yace, Na miki alqawari amma banda sadaukar da lafiyarki ko rayuwarki meyasa z...... Rufe masa baki tayi cikin wani irin yanayi tace, Mu barwa Allah zabi zai mana mafita. Amatuqar wahalce ya taimaka mata ta shirya sbd tuni alummar mineelik da kewayenta suka hallara sbd mahimmin saqon daza'a bayyanar garesu. Duk yanda yakeson daurewa kasawa yayi lokacinda zasu shiga inda dukkanin jama'arta zasu ganta jawota yayi ya rungume da qarfi cikin rawar murya yace, Kisani har abada bazan saki hannunkiba zamu fuskanci duk abinda zai tunkaromu atare, ummu-rumanah bulama kece zuciyar maheer abdulshams so please fight this battle for my love... Ajiyar zuciya tasauke ahankali tareda zamewa daga jikinsa tana riqe hannun ammy dake hawaye gefenta Jakadiya dake gefensu tayi saurin miqawa ammy tissues ganin jinin yanason sake tsananta. Ammy dakanta ta goge mata tana danne kukanta. Murmushi tasaki tareda riqe hannun ammyn ta karbi tissue din tana goge hancinta zuwa bakinta da hannunta dake rawa sbd ko tsayuwa daidai bata iyayi abinda yafi daga hankalinsu kenan. Sultan ma aranar da safe ta bayarda takardar sakinsa dan haka shima tuni ya fito ya halarci taron tareda sauran dattijawon masarautar duk da ayau jikinsa a sanyaye yake da abinda yake faruwar saidai a safiyar yau 'din ya gana da dukkanin 'yayansa dasuka zo dan halartar wannan taro kuma ganinsu ayau din da maganganunsu sun sanyaya jikinsa sunbar zuciyarsa da dana sani musamman maganganun maheer dayayi masa gameda mutuwar iyayen rumanah... Hakan yasa ya ajiye dukkanin makaman yaqinsa akawo qarshen masifar duk da su sunriga sunbi sahu. Tana fita ko ina yayi tsit dukkanin alummar gurin suka nutsu ahankali haroun yabada umarni nan take aka bayyanarda wata irin sabuwar karaga mai tsananin kyawu da kyalli mai daukar ido atake dukkanin jamar gurin mamaki da tsoro yakamasu musamman maheer dabaisan da hakanba yakalleta da sauri saiyaga tana qoqarin danne abinda takejine dan daidaita nutsuwarta yafasa maganar dayayi niyya ya damqe hannunta dake cikin nasa sbd har lokacin a tsaye suke taredasu ammy da jakadiya da masu tsaron lafiyarta. Cikin wata irin budaddiyar murya sarkin fada haroun ya bude wata irin zungureriyar takarda mai daukeda tambarin masarautar mineelik dake daukeda saqon assultana yafara karantowa kai tsaye da qarfin muryarsa yanda kowa zaiji. """" NI SARAUNIYAR MINEELIK UMMU-RUMANAH BULAMA AYAU SHA BIYU GA WATA NA BIYAR A SHEKARA TA DUBU BIYU DA UKU NA SOKE KARAGAR MINEELIK DAN KAWO QARSHEN MULKIN ZALINCI INA GABATAR MUKU DA SABUWAR KARAGA GA WANNAN MASARAUTA...HAKA KUMA AYAU SHA BIYU GA WATAN BIYAR SHEKARA TA DUBU BIYU DA UKU NI UWAR MAGAJI SARAUNIYA UMMU-RUMANAH NA SAUKA KAN MULKIN MASARAUTAR MINEELIK TAREDA 'DORA SABON SARKI ABDALLAH ABDALLAH AMMED"" Atake dukkanin gurin yadauki wata irin kabbara da koke koken farin ciki da sbd wannan wani irin babban alamarine yazo musu na sauyi daga mulkin azaba musamman Abdallah Abdallah ammed mahaifin khaleefa mutum ne dazai kawowa rayuwarsu sauyi na adalci gashi shikansa baisanda zancenba. Tsit aka sakeyi lokacin wasu irin majiya qarfin bayi kusan goma sha biyar suka ciccibo karagar mineelik Wanda keda wani irin girma tareda hularta. Wani irin baro mai tsananin girma da fadi daukeda wani irin mahaukaciyar tukunta mai tsananin tiriri yaran negasi kusan su ashirin da biyu suka turo aka ajiye tsakiyar filin harabar. Ta lumshe idanuwanta dasuka fara rufewa suna gani dishi dishi ta budesu daqyar ta iya 'daga hannu ta bada umarni atake haroun yabada umarni aka 'daga karagar aka saka ciki atake tafara nitsewa tana narkewa cikin ruwan dalmar tun tana gani dishi dishi sbd jinin daya balle hancinta atake idanuwanta suka rufe ruf ta yanke jiki ta zube gurin jini na qarasa balle mata ta hanci da bakinta. #mamuhgee