*_💋SIRRIN DAKE BOYE*_❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌍Destiny, Love❤️‍🔥& Romantic 💋 By Amid💞 2024🔥 Paid book 📚 Bismillah Rahmani Raheem Book 1 Page 📃 1 Gombe ,state Gabukka Tafiya takeyi cikeda nitsuwa daya zame mata Jiki, sanye take da hijab Wanda ya Dan fara kode wa , amma bacan sosai ba , idan ka ganta, zakayi tunanin bata da wani damuwa, amma ita kadai tasan abunda yake damunta , jitake kamar karta koma gidan , Dan ita kadai tasan abunda yake damunta acikin zuciyanta , idan ta koma tasan me zata Tatar, Ajiyar zuciya tayi , Wanda ita kadai tasan tayi, Koda akwai a gefenta ba Lallai yaji ba , ta cigaba da tafiya Kanta a duke, Tana kallan gabanta. Wani gida ta shiga, kana ganin gidan kasan na marasa karfi ne , daki uku ne a gidan , Tana shiga da sallama, babu Wanda ya amsa , wannan ba sabon abu bane , domin kozaka shekara kana sallama , ba Wanda zai amsa , saidai idan , Abba ko zulaihat suna wajan zasu amsa, yan mata ne biyu a wajan, Habiba zaune take Tana kwaliya , Duk daba wani iyawa tayi ba , saidai ba laifi Tana da kyau bacan sosai ba domin a wajan kyakyawa, ita mummuna ce , tsaki Tana Tana cewa mutum ba farin jini ba…., karaf dayar takama mai suna deeje , Ina taga farin jini , sai shegen kyau kamar Aljana , waye zai kwasa abunda zai dagama hankali . Hmmmm adda Habiba kenan, sai sa hijab kaman ta Allah. SULTANA ( strength, authority & rulership) da bata ce komai ba, domin idan da sabo yaci ace ta saba , zulaihat fito wanta kenan ,daya daki ta jisu suna zagin SULTANA , Hana adda habiba , Ku kullum bakinku baya yin shiru , danma ba bari takeyi ba , Tana Mai da muku martani , idan ba ha ka………. , deeje ke zulaihat waya saka bakin ki anan, banxa sai shegen shige ma mutum , habiba muda muke yayunta bata taba bin bayan mu ba , ta fada tareda Jan tsaki Dan abun ba karamin haushi yake ba taba,zulaihat tace , ni ai gaskiya nake fada muku , saboda me sanku ne kawai zai fada muku gaskiya , kullum kuna biye wa Innah, ba gata take muku ba wallahi,Tana fada ta shiga dakinda SULTANA ta shiga , bakinta dauke da sallama ,a tsaye ta samu SULTANA, tana cire kayanta , tana daura zani ( huh 🤔 jama’a kunga abunda na gani?) Saidai kuce tabarakallah Masha Allah, fara ce Tass kaman ka taba jini ya fita, da ka ganta kaga ruwa biyu wait ( halfcast) , danma wahalan rayuwa yasa hasken nata ya dishashe , ga hancinta straight kaman pencil,ga wani (thin lips) dan karami me shegen kyau, me heart shape , omo come and see her eyes (light blue eyes ) masu shining, da gashin gira Wanda ya kusa hade wa da Dayan , Masha Allah (black curly hair)nata me tsayi har waist nata ga laushi da santsi,tanada tsayi yar dadai da ita dan bazaka ce mata guntuwa ba kuma bazaka ce mata doguwa ba , A shekaru bazata wuce sha shida (16) years ba, idan ka ganta zakayi tunanin (18)years, Dan, Allah ya Albar Kaceta da , manya manyan boobs, tsayayyu masu daukan hankali, da mazaunai suna Mayan da daukan hankali ga hips,irrin (coca cola), saidai muce Masha Allah , Dan Duk inda mace take takai mace, koda mace yar uwarta ce ta ganta sai ta shagala da kallanta bare kuma namiji lafiyayye. A rayuwanta ta tsani kallo, sheyasa take saka niqab idan zata fita. Ta dago tana kallon zulaihat da tayi sallam,ta amsa da muryanta mai dadin sauraro,kallo daya ta mata ta dauke kanta , Duk da a gidan a wajenta kawai ta ke samun sassauci,Dan ko uban da ya haife ta bai taba bai damu da cinta ko shanta ba,bare ajega sutura , baya shiga harkanta , bayaso taga sun hadu a Inuwa daya , idan gaisuwa ne ,sama sama yake amsa wa, shiyasa bata cika shiga harkansa ba, yanzu sai ya jibge ta. Samun waje tayi gefen kati fansu ,ta zauna ta na kallon SULTANA dake gyara daurin zanin ta , ajiyar zuciya tayi tanajin dama itace me, kyau, hankali, nutsuwa,ilimi, uwa uba kuma tarbiya kaman ba’a gidansu ta tashi ba , Duk da itama Alhamdulillah tanada nata kyan dan bazaka ganta kace ce mata munmuna ba Dan ita Kyan mahaifinta ta biyo wato fulani , Masha Allah, saidai idan aka hada kyanta da na SULTANA na ba,Dan acikin kashi biyar kashi biyu take da shi. SULTANA, kin zoki ki Sami a gaba kina kallona ta fada cike da tsiwa,da mur guda mata dan mitsitsin lips na ta, cikeda yarinta, tana kallan zulaihat,kawar da kanta tayi daga kallan SULTANA tana cewa kekam da neman fada kike ,dama na zone ne na tambaye ki game da islamiya nima inason, Ina zuwa islamiyanan amma innah ta hana,ta fada cike da damuwa ,domin itama tanaso taga tana zuwa makaranta. Kallanta SULTANA tayi,cikin nutsuwa ta, Dan da fa kafadan zulaihat din tana cewa, naki matsalan kadan ne idan aka hada da nawa,kinsan fah sai nayi aiki nake samun kudin da nake zuwa makaranta,saboda Abba baya shiga har kana , bayason abunda ya dangan ce ni,bayan wanan ma bamuda abunda zamuci,wata ranama gagaranmu yake yi,ga innah da shegen San kudi,hasu adda habiba da adda deeje basuda aiki sai bin samari, wata rana fah , har kwana sunayi basu dawo ba,kuma ba Wanda ya damu,ko Wanda zaiyi magana daga ,harshi Abban da ba haka yake ba ,bansan meya canja shi ba, ta fada blue eyes nata suna kawo ruwa, amma basu gangaro ba ,zulaihat ta da fata tana cewa addu’a zamuci gaba da musu Allah yasa sugane wannan hanyan ba madaidai ciya bace,tunka fun suzo suyi danasani Mara amfani, ta kare maganan dajan tsaki,tana yasuna kyakyawan fuskan ta. Dago da idanta zulaihat tayi,tana ganin SULTANA, ta fara cewa , kullum sai innah tace mana mu Nemo mata kudi kota halin yaya ,bata tunanin wannan ya zama babban matsala Nan gaba,Allah yasa mu dace ta fada tana fita daga dakin ,SULTANA ta amsa da ‘’Ameen’’. (Somin tabine wannan kada Ku bari abarku abaya, domin da zafinsa 🔥 yazo Hh😂) 2024/2025🔥 By Amid✍️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌎Destiny, Love❤️,& Romantic 💋 Written By Amid💞 2024/2025 🔥 Bismillah Rahmani Raheem Paid book 📚 Book 1 Page 📃 2 Daukan wani, kodaden hijab tayi tasaka , ta dauki kondan wankanta ta futa daga dakin. A tsakar gida ta samu adda habiba da adda deeje suna ganin ta suka fara kanamun maganganu, bata kula suba dan bata mode in biyewa shirmensu, daba abunda zai hana bata maida musu da bakar maganar da sukeyi ba. Tafiya tayi wajen rijiyan gidan ta oba ruwan ta shiga wanka,bata wuce 30mins ba tafito , tare da dauro alola , direct dakinsu ta wuce , tana shiga ta cire hijab in data saka da zata shiga wa ka, daga ita sai daure kirji , Mai ta dauka tana sha fawa dan yakusa kare wa ma ,tana gamawa taje wajen kayanta , A wani akwatin auren maman ta ne,dogon riga ta şaka , wanda bashida nauyi, amma ya fara kodewa, yayi mata kyau dan irin matan nane duk abunda sukasa saiya musu kyau,hijab ta saka Wanda allamun sabone,shimfida sallah ya , ta tada sallah, a nustse takeyi, da bin ka kaidodin sallah, harta idar. Cikin gida ta fito,ta daura girki , domin idan na ita ba , ba meyin girki, gwanda ma zulaihat tana tayata idan ta dawo daga talla da wuri,shima idan innah batanan, idan batayi bakuma ta jibge ta San ranta , saikace ita kadai ce mace a gidan, bayan akwai yayun ta har biyu a gidan . Cikin kankanin lokaci ta gama girki dan icen yanada kamu, tazo ta hada kwanika wanke Wanke shima tayi,tana gamawa tayi Shara dan lokacin har an fara kiran sallan magrib. ——————————————————————/——-//—////✈️🛩️ USA 🇺🇸 Zaune take a office nashi Mai girma daya kawatu sosai da kayan more rayuwa dan dollars tayi kuka a office in , idan na tsaya fada muku yanda aka kwawata office in ma zamucinye rabin littafin bamu gama fada ba. Kana ganinshi kaga bature ko ince balarabe, Dan farine tass kaman katana jini ya fito, hancin shi kaman pencil , ga idonshi (ash eyes) masu kyau , sajen daya zaga ye fuskan shi. A shekaru bazai wuce , shekara ashirin da takwas (28) ba, Kana ganin yanda ya dukufa yana duba file in kasan abine Mai muhimmanci takeyi, nocking sai da yaja yan seconds ya bada umarnin a shigo , Duk da hakan bai dagoba yaga wanda yashi gonba. Matashi ne wanda shima bazai wuce wanda saba, Dan they are age mates, zama yayi a kujeran dake passing na table in, yana fuskan tanshi tare da cewa, ‘’ash’’ Kai har yanzu baka gama aikin da ‘’BOSS LION’’ ya Baka ba ( karkuce ban fada muku ba da American English suke magana) . ‘’Ashman’’ kamun magana mana dan kaga zo Ina maka magana kake kyaleni, Hmmm dan ma duk miskilancin ka maka baka kama kafan ‘’ BOSS LION’’ ba domin Kuwait nun kaka ya shanye a toh , Yana mamakin miskilancin shi dan na yau yafi na ko yaushe . Domin shi mutum ne me faran faran , ba kaman ‘’ BOSS LION’’ba. Mikewa yayi da nufin ya bar Mishi office nashi,gyaran murya wanda aka kirashi da ‘’Ash’’ yayi, a hankali ya bude ba kinshi yace ,Hmmm bakasan meyasa nayi shiru ba Dan karan kanka ka sani’’BOSS LION’’ baya daukan nonsense, gashi ban karasar da aikin daya bani ba kasan zaiyi punishing inane , dan wallahi babu ruwansa dani kanin sane, ya karasa maganan cikin damuwa, dan ya sani muddin be karasar akan lokacin daya basa ba akwai matsala, dan su a rayuwansu kowani minute yanada muhimmanci a garesu ( ba kaman yan Africa ba Dan , akwai su da iya African time) Ajiyar zuciya farouq ya sauke yana cewa, shiyasa kagani ko daga ne sane banason wani abu ya hadamu , dan wallahi duk ranan da aka ce abu ya hadamu, da kyar zuciyata ta iya dauka dan wallahi mugun tsoron shi nake ji, dan ni bansan ma , yakuke iya rayuwa ba dashi a gida daya ba. Hmmmm kaga farouq, bashine na tambaye ka ba abunda na tambaye ka daban,Dan kasan jibi zai dawo daga Dubai kuma ka san yadawo, bangana aikin daya sakani ba. Toh wai Kai sai kana abu kaman ba soja ba haba dan Allah, kawai ka Bari ka karbi punishment naka mana, ya karasa maganan cikeda tsokana yana murmushi, ‘’ash ‘’ kuwa wani banzan kallo ya wulla mishi , irin na baka da hankali. Amma dai sanin kanka ne punishment nashi ba Mai sauki bane dan sai yaga ka kusa sumewa tukun Nan zai barshi ya karasa magana yana bin farouq da banzan kallo, da yake mishi dariya. Sorry friend, kawai kayı kokarı ka gama mishi abunda yasaka ka , dan sai yafi maka wannan maganan damuke yi, ya karasa magana da tashi ya fita daga office in dan ya bashi guri ya gama abunda zaiyi. Yana fita ‘’Ash’’ ya maida hankalishi wajan abunda yake yi, dan yanada muhimmanci. —————————————————————-/——//———////🌚🌝 NiGERIA 🇳🇬 Gombe state Zaune take a daki dan idar da sallanta kenan , bayan tagama aikin gıda, gashi yunwa take ji gashi bata isa tasaka abinci ba , dan inhar tasaka tana gane nawa dan akwai ranan da ta iba abinci bata sani, duka ta mata bana wasa ba , dan makwafta sunema suka karbeta ,idan ta tashi sakamata baya wuce loma hudu Shikkenan kuma ,shima saboda karbe kudin aikinta takeyi wata yana cika zatace taje takarbo kudin Tabata. saidai abunda innah bata saniba , a gidan masu kudi take aiki ,dan aikinta shine girkin rana,dana dare na zamanı dan da farko shara da wanke wanke takeyi , toh suna shiri da Mai girkin dan idan ta gama nata aikin , sai taje suna hira suna girkin to anan ta koya girki kuma Alhamdulillah idan tayi girki kowa sai ya yaba harda makiyanta . Toh me musu girki saita fara rashin lafiya tadaina zuwa, itakuma ta koma yin girkin, ko wata batayiba Allah yayiwa mai girkin rasuwa,kawai sai ta cigaba da girkin.da farko Ana biyanta dubu takwas(8,000)sai innah ta karbe , tanajin takaicin wannan abun, saidai Allah cikin ikonshi data fara girkin bawandata fada masa Ankara nata kudin albashi, dan albashinta yafi nada, dan dubu goma sha biyar(15,000) ake bata. Innah ta tsaneni sosai , tsana mafi muni, dan taki Janina, ga takaicin Nafi yayanta kyau nesa ba kusa ba, dan indai wata acikisu adda habiba da adda deeje zaizo da nashi saurayin ta , sauketa , idan aka samu akasin lokacin dawowa na gida yayi nakan hadu dasu a kofan gida, muddin suka ganni , cewa zaiyi ni yake so to wannan abun yafi komai Kona musu rai. Kwanciya tayi a gefen katifan ta kasa, dan katifan ya musu kadan , shiyasa suka Kore ta , dan su uku suke kwana a katifan , dan ita kobasu koreta bazata iya kwana cikinsu ba Dan in suna bacci kaman sun mutu gadaurawa mutum kafa da gwarti duk sunayi, shiyasa takeyi shifi dinta a kasa tayi kwanciyan ta . Addu’a tayi ta tofa a jikinta , tayi bismillah ta kwanta dukda yunwan da take ji, bata jima da kwanciya ba bacci ya dauke ta Dan a gajiye take . Asuba ta gari 😴 —————————————————————-/——-//———////🌈 USA 🇺🇸 Har yanzu yana zaune an office yana tattara takadddun da zai tafi dashi gida , dan a cen zai cigaba da aikin, dan a gajiye yake wallahi , amma yasan halin ‘’BOSS LION’’ ba wasa. Tashi yayi tsaye , Masha Allah, dagone karfafa, yanada faffadan kirji, gashi kakin yamishi kyau, sai yatsuna fuska yake yi , dan bakarya yagaji, cikin kankanin lokaci ya gama harhada abunda zai dauka ya fito, yana fito wa wani soldier ya Sara mishi hade da karba abubuwan hanun shin, wasu kuma sara mishi suke yi duk inda ya gifta, hannu kawai ya daga musu ,daidai lokacin da lifts in ya bude shiga yayi sukuma sauran suka shiga wani lifts in dan suriga shi fito wa . Lifting yana bude wa sauran sojojin duk suna tsayi suna jira sakko wanshi da wannan umarnin’’BOSS LION’’ ne Suna fita compound in suka samu , wasu zuka zukan motoci masu numfashi guda biyar , bude mishi motor tsakiyan yayi yashi ga soldier ya sara mishi yana rufe motan, sauran hudun sun saka shi a tsakiya , gudu suke yi amma ba can sosai ba . Wani arnen anguwa suka shiga, anguwani irin na masu hanu da shuni , irin harsun rasa ya zasuyi da da kudinnan, Wani makeken gidan naga sun tsaya ,wanda kana gani kasan anguwa gudane wannan gıdan, wooooooo hohoooo😲😳, get din gidan kadai abu kallo ne , anyi mishi wani design kaman da gold akayi shi , dan yayi masifan kyau , sojoji ne abakin get suke gadin gidan. Get din aka bude musu suka shiga, Hmmmmm wato sojojin da suke first get ba komai bane , idan aka hada da wanda suke second get , akwai tafiya mai tsayi sosai, dan second get da kanshi yake bude wa , a jikin get in akwai na’uran daya ke screening din plate numbers din motors in da wanda yake dauka pics din motor shima sai yayi screening kafun get din ya bude ( duka duka baya wuce 10 seconds yake budu wa . Cikin haraban kata faren cikin gida ,suka shigo , idan nace muku kata fare gida ne daya amsa sunan sa gida wanda mutane suke cewa aljanan duniya Kenan , dan wanda baisa addini a zuciyan saba , zai kafirce dan zai iya mata wama da menene sallah( Allah yasa mu dace)gida ne anguwa guda dan wallahi ko gidan sugaban kasar albarka, gıda ne daya kawatu da kayan more rayuwa . Glass ne daya amsa sunan sa glass Wanda yayi millions of dollars 💵 glasses ne ma kyau da daukan ido ( kunsan turawa iya tsara abubuwa . ( Hmmmmm wannan dai sai munayin gaba a karatune , Zan Ina kwatanta muku yanda gidan yake domin idan nace zan tsaya fasalta muku yanda gidan yake zamu kare littafin kaf , bamu karaba) 2024/2025🔥 Written by Amid✍️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌎Destiny, Love ❤️& Romance 💋 Written by Amid💞 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Book 1 Page 📃 3 A bakin screen door din ya tsaya ,daga bakin kofan daga shi sai sojan da ya dauko mishi file,da system nashi suka shigo, suna shiga wani kamshi da sanyin A.C ya dake su , harda lumshe idanunshi, ya bude akan wani saurayi da bazai wuce (23)ba sanye yake da jeans da t-shirt masu tsada, kana ganin shi kaga brother nashi ne domin suna kama ,gashi kyakyawa (brown eye )👁️ nida shi masu daukan hankali, black hair shi ya sakko har kusan kafadan shi da yana tara gashin. Rungume juna sukayi ya na cewa, ‘’Brother ash’’ welcome back, hade da sakarwa juna kiss a kumantun juna ,how was the work,Alhamdulillah, ‘’Ash’’ ya fada a hankali. Karban files din dake hanun sojan yayi,’’ Ash’’ yaba gaba, junior yana bin bayansa , har suka kara sa cikin main falon gida,wato wasu shegun kujeru ne masu shegen kyau da tsada , kujeru set hudu ne a falon ,milk color,brown,ash with golden color,blue with white ,with their king chairs , dan girman falon Kai ya ninka wani gidan,ga wasu blackout curtains masu kyau daya kawata falon, samsung’s television me girman gaske ga decorative roses 🌹 flowers 🌺 da,a ka jera a saman center table, Masha Allah komai mai kyau ne me tsada kuma nayayi dan every 6month ake tanja komai na gaidan. Wajen lifter suka tsaya,cikin sauri junaid ya dan na Hawa uku(3), shiga sukayi tare , within seconds lifter n ya bude , jerawa sukayi suna tafiya ba Mai magana. Cikin wani falo suka shiga, yananada girma amma bai kai main falon gima ba, direct bedroom suka shiga daya saha kings bed mai kyau da ban sha,awa, ayiye mishi files din junaid yayi ya juya. Junaid Tana fita ya rage Kayan Jikin shi , yashiga wanka bai wuce 30mins ba fito , dressing room yashiga , pajamas ya dauko blue color,falo ya sakko, wuce wa yayi dining area , Sara mishi sojan dake tsaye a dining sukayi saving nashi ya yi,chikin kankanin lokaci ya gama cin abinci dan baya wasa da cikin sa. Yana gamawa ya dauki system nashi ya fara aiki,sai wajen 1:00am ya tashi duk da hakan bai gama ba ,daki junaid ya wuce domin du bashi ,addu’a ya masa , danshi Kwata kwata bayansan yin addu’a , duk da ya iya amma bazai iya yiba, dan ko yayi niyan yi sai wani abu Tasha mishi kai ya manta. Dakishi wa wuce ya kwanta dan aga jiye yake shima. ———————————————————————/——//——////💐 Gombe state Kiran sallan farko ta tashi , ta fita tayi alola, shimfida sallaya tayi , ta fara nafila da kuma raka’a tanıl fakir sukuwa adda habiba da adda deeje harda zulaihat bacci sukeyi dan wani lokacin ma kota tashe su barazu tashi ba saidai sufara mata masifa shiyasa ta daina tashinsu,kullum a makare sukeyin sallah , wajen takawas ko tara , suke tashi suyi sallah , har zulaihat in dan itama a kwai nauyin bacci . Tana idar da sallah tafiya waje ,ta kwaso buckets 🪣 da zata iba ruwa a rijiya ,ta cika duk randan gida, wanke wanke tayi bayan ta gama tadaura musu koko , dan yau babu wani abun a gidan ida ba kamun kokon ba . Bayan ta gama ta iba ruwa tayi wanka dukda yunwan da yake cinta , Tana fito daga wanka ta shafa mai ,da powder amma ba sosai ba dan kadan, dan ba lallai mutum yasan ma ta shafa ba ,kwalli ta saka da lip glows ta bude akwanti n, ta dakko a tamfa me kyau nevy blue ,Masha Allah dan yanda kasan dawisu haka take yalki ,hijab ta dauko shima nevy blue,da niqab nata tayi kyau,(ohhh my god 🤗) Fito wa tayi daga dakin,bakin dakin innah tawuce , sallama tayi har sau uku ba’a amsa ba, kuma tasan sarai taji amsa wane kawai bazata yiba, bata gama tunanin zucin ba Yaji muryan innah , tana surfa mata masifa, ke , dallah matsamun daga bakin kofar daki , ta fada cikin daga murya SULTANA cewa take innah Ina kwana, cikin masifa innah tace , daban kwana ba zaki gannine dan ubanki da fuska da fuska irin ta aljanu , ba zaki daina kallona da wannan yan iskan idanu yawana mage ,SULTANA cikin dan bacin rai ta ce , innah fita Zanayi, kuma baki banı kokon ba ,’’ dan ubanki bazan bayarba,fitsararriyar yarinya kawai ,Watarana sai zaman gidannan ya gagare ki wata Rana indai Ina raye , ta karasa maganan tare da huhura hanci , tana binta da kallan tsana. Itadai SULTANA,dama batayi tsammanin zata bata abinciba,duk da kuwa ita ta girka,domin ba sabon abu ba ne a wajen ta ,sai taga dama take bata abinci. Sum sum tanufi hangar waje,tazo fita, abba kuwa ya zo shiga ,dan bayan dawowanshi daga sallah ankira shi wai wani yana sallama dashi a waje,cikin muryanta mai dadi tace,Abba Ina kwana ,banza yayi da ita kaman bai ganta ba ,dan idan ya ciga ba da gannin ta zai iya dauke ta da Mari ma. Ganin bai kula ta ba , fita tayi daga gidan ,dan wannan bai dame taba,tafiya take yi a hankali cike da nutsuwa ,tayi tayan awa daya da rabi ,kafun ta iso GRA ,dan Dani sa. ———————————————————————-/——//——////🤪 Abuja/Nigeria🇳🇬 Asokoro street Wani gida ne mai kyau na zamani,falo ne mai gima daya wadatu da kayan more rayuwa. Babbar macece zaune a kan kujeru na alfarma dake cikin falon ,a shekaru bazata wuce 48 years ba , A duniya idan kaganta zakayi tunanin bazata wuce 38 years ba, gata black beauty ,alamun jindadi da kwanciyan hankali ya Wada ce ta,azkhar ne a hanun ta ,tareda carbi,addu’o’in marai ce take yi. Wata yarinya ce ta sauko da gudu daga up stairs bazata wuce 15 years ba kyakyawace black beauty,tanada dara daran idanu (brown eyes) kaman madara,tanada jikin girma masha Allah . Fada wa tayi jikin wannan matar tana cewa , Ammi wai yau yaya alameen zai dawo , tafada tana yatsuna fıska , cikin kulawa Ammi tace eh yau zai dawo,bata fuska tayi,wallahi dama kar ya dawo,dan yana dawowa zai fara takuramun ta fada cikin rashin Jin dadin dawowan sa . Ammi kuwa tsaya wa kawai tayi tana kallan ta ,,ta rasa meyasa basa jituwa da juna ,saikace ba ciki daya suka fito ba,da fata Ammi tayi da cewa karki damu bazan bari ya miki wani abun ba’’ tab Ammi kenan kina Ina zai mun,mguntar daya sa………….,maganan tane ya makale Jin sautin sallamarsa kaman saukan aradu haka taji,shigo wa yayi hanunsa rike da ludge nashi mai kyau yanaja,kuma tsaf yaji abunda take fada,saurayi kyakyawa farine amma ba tass ba yanada tsayi bacan sosai ba ,gashi bashida jiki sosai,saidai yanada faffadan kirji. Cike da farin ciki Ammi tace ,lale mutanen Morocco 🇲🇦, cikin sakin fuska da ladabi ya ce ‘’ Ammi Ina wuni ,nasa meku lafiya,lafiya kalau ya hanya,,Alhamdulillah,yace yana mai Jin farin ciki idan yana kusa da maihaifiyarsa. Cikin dake wata ce yaya alameen,Ina wuni,ka iso lafiya,,cikin basarwa yace lafiya yace lafiya tare da mikewa yace Ammi bari nadan watsa ruwa na fito, a fito lafiya,,yace Ameen ,, dakine mai kyau daya sha (Italian bed) white and brown,sanyi ac ne da kamshin air freshener,yana shiga ya cire kayansa ya daura towel,yashiga toilet 20mins ba ya fito yana tsane jikinshi black three quarter,da t-shirt white yayi kyau ya fito da Kya wunsa na asalin bafulatanin sa, feda turare yayi masu dadi,, fito wa yayi yana tafiya a hankali,cikin falo yashigo . Bai samu Ammi a falo ba sai shukra da ya gani ,zaune kana kallon Zee world , Kara sowa yayi wajen wajen kujeran ya kira sunan ta, amma bata jiba dan tabada Duk hankalin ta a tv,,bubbuga kujeran yayi fuska a daure yace ‘ke meyasa bakida hankali ne ,,eh ,,ya fada cikin tsawa , cikin sauri tace yaya alameen kayı hakuri banji bane ,kwafa yayi irin na zaki sanine. Muje kiyi saving Ina ,cikin sauri tace Toh,,dan ita tsoronta karta taba mata lafiyan jikin ta. Gaba yayi tana binsa a baya tana turo baki gaba,kan dining area ,Jan kujera yayi ya zauna ,,cikin rawan murya ta ce yaya alameen meye za’a saka ma, cikin halin ko in kula yace everything,, pride rice da chicken pepper with zobo mai sanyi,tura masa gaban sa tayi,spoon ya dauka ya fara ci cikin kwanciyan hankali dan abincin ya mishi dadi sosai, juyawa tayi zata tafi,ki zauna idan na gama ki kwashe kwanukan,,Toh tace Taja kujera ta zauna tana jiranshi ya gama cin abincin,,bai wuce 20mins ba ya gama ,,mikewa yayi ya shiga dakinsa dan anfara kiran sallan magrib. Ita kuma tattare kwanukan tayi tana magana kasa kasa harda mur guda baki,tana gamawa ta wuce dakinta tayi sallan magrib da isha,fito tayi daga daki tawuce dining area anan ta samu,,Ammi da Abu sunacin abinci,,yaya alameen kuwa yana dawowa dakinshi ya wuce ,,kwanciya yayi dan a gajiye yake. Dan Allah,anayi likes da comment 2024/2025 🔥 Written by amid💞 *_💋 SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌎Destiny,Love❤️& Romance 💋 Written by Amid✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Book 1 Page 📃 4 Abinci take ci a hankali ,ita kadai ce ta rage a dining table din,dan Ammi da abu sun mata saida safe. Itama tana gamawa ta tattare wajen ,ta haura dakin ta ,tana zuwa ta cire kayanta ta daura towel ,wanka tayi tafito ,shirya wa tayi ciki riga da wando pink color masu da laushi tayi addu’a ta kwanta. ———————————————————————/——//——////🇳🇬 Gombe state GRA Anguwane ta masu hanu da shuni ,gida jene masu kyau a anguwa. A bakin wani get ta tsaya, dan gidane mai girma ,saidai bacan sosai ba ,cikin gidan akwai up stairs da kuma normal flat guda biyu , daya na boyz quarter ne dan yafi dayan part din girma sosai,Dayan flat din gefen masu aiki ne ,daki biyu ne a ciki. A hankali take tafiya har ta’isa bakine entrance din dazai sadaka da babban falon gidan, bude wa tayi ta shiga da sallama a bakinta dan lokacin large 8:30 ne , dan da safe take zuwa,dan daura abincin safe. Bata samu kowa a falon ba,sai dai alamun an gyara falon da n kamshi be ke tashi, Direct kitchen ta wuce ta samu Tana daura musu abincin karyawa dan yau chips with egg source take so tayi. Cikin kware wa , ta fara fere dankalin ,dan da yawa akeyin abincin gidan ,dasu masu aiki da masu gadi ,dan mai gidan mutum ne mai dattako da kyauta . Tana fere wa take soyawa ,sai fast 10 tagama, dan gidan yan boko ne sai sunyi baccin safe ,dan wani lokacin ma sai sukai 11:00am basu sakko ba , tana gamawa ta zuba a flask masu kyau ta kai dining table ta jera su ,komasa kitchen tayi ta zuba abinci a sauran masu aikin gidan suma. Diban nata tayi, ta zauna tacı tayi nak ,tace Alhamdulillah,dan rabonta da cin abinci tun jiya a gidanan. Tana gamawa ,sai lokacin ta farajin hayaniya yan matan gidan ,cikin nutsuwa ta fito daga kitchen din ,dan tazo tayi saving nasu abinci. Tana zuwa ta samu har mami da daddyn Aneesa suna zaune dan zuwansu Kenan ,yan mata biyu ne da samari biyu , dake zaune a dining table din. Tun daga nesa taga irin kallan da Zainab ta ke biya dashi ,kallo ne irin ta tsana take mata, ta gefen ta kuwa Aneesa ko kallata bata yiba,sai maza biyun da yan na wulla mata kallo irin na yan iskanan,mai suna jabir. Gaishe dasu mami da daddyn Aneesa ya fara yi , amsa mata daddyn aneesa yayi cikin sakin fuska amma banda mami ciki ciki ta amsa ,sannan ta gaishe da ya mujahid da ya jabir,amsa mata sukayi ,jabir yana wani karshe mata ido daya irin na tantiran yan iskannan ,tukun ta gaishe da zainab da aneesa duk da dai zasu iyayi sa’ani da aneesa . Cikin kankanin lokaci ta zubawa kowa nishi ta tura mishi gabansa ,suka faraci,ita kuwa kitchen ta koma ta daura abincin rana dan har 12 tayi. By 2 tagama shima taje ta jera musu a dining ,kafun ta koma kitchen domin daura abincin dare, shima by 4:50 ta gama taje ta jera musu na Daren dan ,tagama aikin ta na yau ,hijab nata ta gyara tareda daura niqab nata,tayi mawa sauran masu aikin saida safe. Tafiyan awa daya da rabi tayi ,kafun ta isah gidan,dan lokacin har an fara kiraye kirayen sallan magrib,da sallama ta shiga cikin gidan saidai bata tarar da kowa a gidan,sai takalmin innah data gani a bakın kofan dakinta,ajiye abincin da tazo dashi tayi ,wanda na ranan tane ta bari ta ajiye sai ta dawo gida taci, tana shiga dakin nasu ma bata samu kowa ba , fito wa tayi ,tayi alwala ,tayi sallah tukun sai lokacin taji sallaman zulaihat take shigo wa gidan dauke da kwanikan abincin sayarwa tana ganin,SULTANA ta sakar mata murmushi, itama mai da mata da martani tayi ,Masha Allah kunga madarar kyau kuwa dan har beauty points nata sai da suka lotsa,Tabarakallah. Zulaihat kuwa direct dakin innah taje, SULTANA kuwa daki ta koma dan yau bazai yuwu tayi Shara ko wanke wanke ba ba ,daki ta shiga taci abincin ta ,takoshi ta wanke hanun ta ,ana kiran sallan isah ta , tashi tayi salla ta ,tayi shimfidan ta ,,ta yi addu’a kwanta . Sai lokacin Adda habiba da adda deeje suka shigo ,tana jiyo yanda suke ta zagin junan su,cikin kankanin lokaci bacci ya dauke ta . ———————————————————————-/——//——////🥰 USA 🇺🇸 Washe gari 7am ya fito zuwa ,office dan ,an musu kiran gaggawa ne, yasa ya fito, gashi bai gama aikin da ‘’ BOSS LION’’ ya bashi ba ,ji yake yi kaman yayi kuka wallahi dan bayasan abunda zai ha dashi da ‘’BOSS LION’’ . Yana fitowa ,sojojin suka fara sara mishi ,daga musu hannu kawai yayi,direct wajan da aka parker motocin nasu yaje ,wannan sojan mai suna john Sara masa yayi hade da bude masa matan ,shiga yayi suka fita daga Gidan straight. Basu dawo ba sai 8pm na dare suka dawo gidan,kuma har lokacin bai samu ya Karasar ba dan shi har ya sadakar sai yayi sai yayi punishment din’’BOSS LION’’ dan ba’a karya mishi doka. Ruwa kawai ya watsa yabi lafiyan gado,dan kar ya makara zuwa ,dan zuwa karfe biyar (5am) jirgin ‘’BOSS LION “zai saka ,immediately after fajr prayers,jirginsu zai sauka ,shiyasa yake san ya kwanta da wuri dan ya dauko shi akan time ,idan ba haka ba kuwa ,ransa idan yayi dubu Toh zai baci. Asuba ta gari mutanen”Ashman”✌️ _____________________________________________*✍️ Abuja Kiran sallan Asuba ne ,ya tashe sa daga baccin gajiyan da ya dauke sa , ban daki yayi alwala ya fito, masallaci ya tafi, bayan an idar da sallah ya dawo gidan. Dakisa ya wuce,zama yayi ,yai azkhar da karatun alqur’ani mai girma ,lokacin har Safiya ta farayi,kafun ya rufe qur’an ya kwanta ,yana kwanciya kuwa bacci ya dauke shi. Shukrah kuwa ,Ammi ce ta tashe ta ,tayi sallah Asuba ,bata koma ba dukda kuwa yau Monday akwai school ,amma bata ra’ayi zuwa school yau ,shiyasa bata tashi ta shirya ba ,baccin Tama takoma. Sai wajen fast 10 tukun ta tashi,daga bacci,a gurguje ta shiga wanka tafito,atampha me design na leaf,pink and purple ,sanan ta daura dankali,daurin Zara Buhari, tayi kyau ,black beauty skin nata dake ta glowing yana shining. Falo ta fito,at the same time,shima yaya alameen ya shigo falon, Ina ganin shi bansan time din dana ci wani uwar burki ba,dan wallahi kwata kwata na matan da yadawo gidan. Shikuwa alameen da mamaki yake kallan ta dan yasan dai yau Monday ne,kuma akwai makaranta, ranshi ba karami baci yayi ba dan yasan wannan laifin Ammi ne ,dan ta ta daure mata gindin zama, amma in Fasu san wata ba ,zasu san wata. Cikin hade Gira yace ,ke shukrah meya hanaki zuwa makaranta “ammm wallahi ya alameen kaina ne yake mun ciwo shiyasa banje ni ba” ke ni sa’an wasanki ne da zaki fadamun wai kanine yake ciwo shiyasa baki je makaranta ba,”marairaicewa tayi tace ya alameen da gaske nake fah. Gaga sama yaji murya Ammi Tana cewa, wai alameen meyake damunka ne,inadai tace maka bata da lafiya ne,ai zan ce ya kare, ni bansan me yarinyar Nan ta tare maka ba wallahi, ta fada Tana nufah daya daga cikin kujerun falon ta zauna. Shikuwa alameen dama yasan za’a rina,dan wannan ba sabon Abu bane a wajenta bai san meyasa ba muddin zata yi fada a. Shukrah indai Tana wajen fah,bai isa mata ba. Cikin warning ‼️ ya kalla shukrah da haryanzu take kalan sa yace wallahi nan gaba muddin ,kika ki zuwa makaranta haka kawai,wallahi ranki inyayi dubu to zai bace, kinjin ko “kanta ta gyada mishi”cikin fada fada yace, Ina miki magana da baki ,zaki wani dagamun kai ,yanda na miki magana da bakai haka zakimun " Toh tace, insha allahu hakan bazai kara faru ba"good yace dukansu suka tafi wajan dining cin abinci. 2024/2025🔥 Written by Amid✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌎Destiny,Love ❤️‍🔥& Romance 💋 Written by Amid ✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Book 1 Page 📃 5 _____________________________________🌹 USA 🇺🇸 Karfe hudu(4am)ya tashi sallan asuba, alwala ya dauro, kafun ya sauka first floor ,anan ya samu junaid ,uncle İbrahim da uncle tareeq a zaune suna jiranshi ,yana zuwa suka wuce masallacin dake gidan, dansu yau babu wanda yasan yau “BOSS LION “ zai dawo ba. Suna fitowa daga sallah ,suka shigo cikin gida , cikin sauri “Ashman “ya shiga dakinsa,domin shirya wa ,dan jirginsu ya kusa sauka . Shaf shaf ya shiga wanka ,bai wuce 10mins ba ya fito dan kar yayi latti,shirya wa yayi cikin kakansa na sojoji ,dan ya farajin karan helicopters 🚁 sunata shawagi, wannan yana nuna musu cewa mai gayya mai aiki ,zai dawo wato “FIELD MARSHAL “ zai dawo kasar .(zakin fama maija da shi sai Allah ). Fito wa yayi daga daki cikin sassarfa,ya fito main falon , anan ya tarar da junaid dake tsaye yanata zazzare ido alamun ya nuna ya mishi laifi,sauran uncle İbrahim da uncle tareeq suma da suke tsaye dan cikinsu ya dura ruwa .Dan wannan karan helicopters din ,yana nuna fah “FIELD MARSHAL “ nanan ta fe🤪 Bai bi takansu ba ,waje ya wuce ,dan lokacin it already 4:40am ,duk sojojin a shiye suke ,suma cikin kakinsu ,dan suma kana gananin su kasan hankalinsu a tashe yake ,sai dai kawai dake wa irin na sojoji bazaka taba gane waba. Cikin motocin suka shiga,dan sun iba motoci sukai guda goma sha takwas (18) dan dakko “FIELD MARSHAL “ gudu suke shararawa a hanya,shiyasa suka isah dawuri,dan lokacin time 4:56am , dan sai 5:00 jirginsu “FIELD MARSHAL “ zai sauka. Fitowa sukayi gaba dayansu,daga cikin motocin , har da “Ash” dake tare da abokin sa farouq,suna tsaye suna magana ,karan saukan jirgi ya karade kunnuwan su,A hankali jirgin ya sauka. Private jet 🛩️ ce mai shegen kyau da tsada ,a jikin jet din an rubuta , “BOSS LION “a ka rubuta a jikin jet din da manyan harufa masu style,kana ganin jet din kasan ba karamin billions of dollars 💵 aka karshe wajan kera taba, dan ya hadu ne iya haduwa, wai dan ma bamu shiga daga ciki ba. Bayan yayi landing,baifi da five minute ba ,wasu jiga jiga sojoji ne wa yanda suka amsa sunan su sojoji suka fara dauko wa ,dan sukai su goma sha biyu ,hakanma mai gaiya mai aiki cewa wa yayi shi kai zai je amma Ina ,mutum ne mai muhimmanci d bazasu iya barinsa ya tafi shi kadai ba . (Bari na leka muku cikin private jet ✈️ din naga meye ne aciki,dan gulma na cina 😂) Wani saurayi na gani zaune akan kujera masu kyau ,a zaune yake yayi crossing legs nashi ,Baka iya ganin guskan sa dan akwai face marks a fuskan sa da kuma glass no respect,ga shin sa daya sha gyara(black curly hair) ,dan kana ganin yanda gashin yake yalki ,zakasan ba karamin kudi a ke kashewa gashin ba,dan ya sauko har kan fuskan sa,kana ganin sa kaga ingarman namiji , namijin daya amsa sunan sa namiji ,dan wasu matan suna suka tara . Kansa jingine da jikin kujera,dan idan kagansa zakiyi tunanin bacci yakeyi ,yakai kusan 20mins a haka,kafun ya mike tsaye ,irin mazan nane masu tsayi,dan dogone ba karya dan jikin sa a murmurde yake ,kana ganinsa kasan ya mishi da training,dan wallahi irin wayanan ka kuskura wani Abu ya hadaku Toh sunan ka sorry 😢, Sanye yake da wane black jeans da t shirt na gucci ,ya daura jacket a jikin Kayan,Kayan sun yi mishi wani shegen kyau,Kyan da idan aka ce kyau Toh ana nufin kyau,dan kayan ya fitar da asalin kyau shi,kana ganinsa kasan bazai wuce ,talatin da biyu (32) ba a duniya. Tafiya yake yi cikin kasaita,irin na jarumin soja da mututanen da suka jika da hutu,ya zauna a jikin sa Fatan sa sai yalki yake yi ,yanda yake tafiya ma kadai abun kallo ne ,dan tafiya ne irin sojoji masu jini a jika. Tundaga nesa “ash”da farouq suka hango sa ,su karan kansu sun sani,bakaramin burgesu yake yiba,cikin sanda farouq yabar wajen da “ash”ya koma can gefe ya tsaya. Sara mishi sojojin suke tayi ,kam zasu yi mishi sujjada tsabar girmamawa,ga yan jarida ma ba’a barsu a baya ba ,dan suma dayawa sukazo,Duk da sunsan ba kulasu zaiyi ba ,hot one shima iya ka cin su dauke sa daga nesa,Duk da har yau acikin 100% baifi 10%ne suka taba ganin fuska sa ba dan koyaushe da face marks a fuskansa. Ga sojoji ta koina dan ko shugaban kasa albarka dan ba Lallai idan zai samu mutane haka ba . Kara so wansa kenan wajen motocin,Sara mishi “ash”yayi tare da kame wa , dan nuna ban girma ga yayansa kuma ogansa a wajen aiki. Yi yayi kaman bai San da halittansa ba awajen,amma sarai yaganshi Jiki da Kai ne kawai. Direct wajen wata shegiyar mota suka nufa ,mercedes -benz GLE 450 4matic ya nufa , cikin sauri “Ashman “ ya bude masa kofan tare da Sara mishi ya rufe, wuce wa yayi,shima cikin sauri john ya bude masa motan dake bayan na “BOSS LION “ din. Wani irin gudu suke yi akan hanyan kaman zasu tashi sama,dan har yanzu garin bai gama waye wa ba ,dan bazai wuce 5:45am ba. _________________________________________________💋 Gombe state Gabukka Washe gari Tana tashi sallan Asuba tayi,tan idarwa,tayi Sharada wanke wanke ,kafun ta daura musu dumamen tuwo ,cikin sauri tagama,ta shiga wanka. Tana fitowa ,ta shiga dakinsu ta shiya cikin material orange color,abunka da farin mutum ta haska kayan,hijab ta dauka ,tasa tukun taje dakin Ina ,Tana tunanin komai zata tarar kuma yau. Gaishe ta tayi Ina kwana ,wai ke kullum sai an mabaki amsa amma dake ke dakikiya ce kin kasa rike wa . Ran SULTANA ya baci amma ta shanye dan tasan idan tanına ita zata sha wahala,cikin sanyin murya tace innah abincin “wallahi wannan yariya anyi jara babbiya ,Toh gashi ki dauka kije,Tana dangwarar mata da roban abincin, dauka tayi taje dakinsu tace ,dan ko kwatan koshi bata yi ba ,Tana gamawa ta fito daga gidan . Tafiyan awa daya da kwata tayi,a hakanma sauri tayi ,Tana zuwa tawuce babban falon gidan, tana bude wa zata shiga ,shikuma zai fita. Binta yayi da wani mayen kallo irin na tantiran yan iskan nan tare da cewa hey baby yafada yana kokarin Tabata ,saurin kauce wa tayi ,tare da balla masa harara da kyawawan idaonta, cikin masifan da tadade batayi ba tace dallah jabir ka fita a hanyata ,idan kuwa Baka fita a hanya taba zakayi danasani. Wai Kai kana tunanin kowa dan iska ne irin ka toh wallahi bari kaji Duk iskan cikinka baka kaini ba dan haka ka fita harkanta ,dan nafi karfin ka ,sai gani sai hange tare da mit guda masa baki da harara babu ko dar a zuciyanta . Shikuwa tsaya wa kawai yayi yana kallanta dan bai taba tunani tanada Baki ba dan kallan shiru shiru yake mata dan bata taba maida mishi da martani ba ,shiyasa yake mata ganin bata da wayo ,Ashe masifaffiya ce, shareware yayi tareda cewa dan halak kafasa ,yabi ta gefenta ya wuce. A gurguje tayi aikinta dan yau tanaso takoma gida da wuri kafun a kira sallan magrib. Cikin kankanin lokaci ta gama aikin ta ,dan yau bata hadu dasu aneesa ba da zainab dan sun tafi makaranta . Zuwa uku da rabi ta gama komai ta shirya wa takama hanyan gidansu. A kofan gidan su ta samu wani, ta kudirin dan daba, yana tsaye yana jiranta, zuwa tayi zata wuce yayi saurin Shan gaban ta yana ce wa , haba baby kinsan lokacin Dana ….. 2024/2025🔥 Written by Amid✍️ 💋*_ SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌎 destiny,Love ❤️ & Romance 💋 Written by Amid✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Book 1 page 📃 6 ___________________________________________🌹 A kofan gidansu tasamu wani, ta kudirin dan daba,ya na tsaye yana jiranta ,zuwa tayi zata wuce yayi daurin Shan gabanta yana cewa haba baby kinsan lokacin dana bata Ina jiranki kuwa gimbiya ta , yanada yake maganan kadai ya’isa ya ,saidawa mutum dan daba ne ,manna mishi tayi ,gimbiya kinsan yanda nake sanki kuwa ,zan iya kashe kowa akanki. Wuce wa tayi gida tabarshi a wajen ya nata maganan da bashi da Kai bare gindi,da sallama ta shiga gidan ,ranta Duk ba dadi. Tarasa meyasa innah takeyi mata haka dan Allah,Shikkenan ita bata daga ta kenan,wasu hawaye ne masu zafi suka sauka a kuncin ta ,saurin sharewa tayi ,dan taji muryan innah tana cewa “toh shi wannan din dakike gudu shi zaki aura ko kinaso ko bakya so wannan din dai shi ,a toh,idan zaki sawa kanki ruwan sanyi,tana fada ,ta cikawa zanin ta iska. Itadai bata kulata ba dan,inta kulata sai abun yazama babba. ______________________________________________😎 USA 🇺🇸 Suna İsa gida , Duk sojojin saida suka fito,suka tsaya suna jiranshi ya fito,yakai kusan 5mins kafun ya fito da kafansa dake sanye cikin booth ,mai daukan hankali,cikin kasaita ya fito daga cikin motan ,abun gonin burgewa. Kai tsaye main falon gidan ya wuce,anan ya samu su junaid a tsaye alamun jiran shigo wansan sukeyi,ko kallan inda suke baiyi ba a cikin falon. Wajen lifter yaje,da Kansa ya danna number 4,hawa na karshe kenan,within some seconds kofan lifter yabude. Fitowa yayi cikin takunsa na ingarman namiji ,wajen wani hadaden kofa yaje,kana ganin wannan kofan kasan dollars tayi kuka ,kofan mai hade de da na’urannane ,da dai kasa password zai bude. Dan babu mai shiga cikin side nasa sai, junaid da Ashman ,su kadai ne sukasan password na door din, shiga yayi bakinsa dauke da sallama ama iya shi kadai tasan yayi ,falone mai girma daya kawatu da ababen more rayuwa, Dan falon Nan ya nunka falon kasa hadu, main falo kawai girma zai nuna masa. Shiga yayi , ko Ina a gyare fess fess sai kamshin dake tashi, wajen wani kofa naga sha shiga ,Ashe bed room ne ,bed room ne mai girma daya kawatu da design masu kyau na furniture’s ash and golden colour,ya matu kar kayata dakin, ga wani center table a gefen mai hade da king shape chairs guda biyu da wani L-shape chair shima a gefe, yayi kyau sosai . Gaban dressing mirror kuwa,perfume ne masu kyau da tsada,shake a gaban dressing mirror,lotions,tissues etc. Shiga yayi cikin nutsuwa ya fara rage kayan jikinshi,tukun ya daura towel a kugunsa,wata kofa naga ya shiga ,daga gani toilet ne,wani irin jacuzzi ne mai tattare da varb ga wani ,long and beautiful drawer,mai cike da kayan anfanin wanka da soap 🧼 iri da kala,har mutum ya tasa abunda zaiyi dashi ,ta gefen kuma towel hangers ne ,mai dauke da towel white colors almost twelve. Ruwan wanka ya hada mai zafi dan su koyaushe kasar da sanyi,ga sabulai da abun kamshi iri da kala ,ga kamshi sai tashi yake yi ,da kuma daya zagaye varb in,shiga yayi cikin ruwa ya Kai almost 30 min a cikin ruwan kafun ya fara wanka shap shap,10mins ya kara kafun ya gama Duk abunda zaiyi ,towel ya daura a kumkuminsa Dayan kuma ya na goge curly hair sa. Fitowa yayi zuwa wajen dressing mirror, wato irin wayanan ko a hanya ka hadu da irinsa to ka canja hanya, dan wani irin murdaden Jiki ne dashi ,daya sha asalin training da daga karfe ,gashi da ffaffadan kirji ga nonuwanan bulbul abunsu,He look dammmn sexy. Lotions ya sha fada sauran abubuwa , ya dauko hand dryer ya busar da kanshi da sha musu mayuka masu kamshi da tsada ,domin hair sannan ba karamin kudi yake kashe masa ba ,taje wa yayi ya gyara shi sai shining yake yi. Mike wa yayi,wajen wani kofa ya shiga ,a haka dai babu komai ,gani nayi ya danna wani remote ,take wajen kayan yabude a cikin glass , kayane masu ya wa ga tsada ,danshi company ne suke buga masa kayayakinsa shida ,Ashman,da junaid. Suits ne kala kala ba kalan da babu daga kan dark color and lights color masu tsadan gaske irin na kece raini ga side na , three quarters , t-shirt,jeans ,vest ,boxers ,p-caps,diamond rings and watches,gold rings and watches,neck tie,shoes,cover shoes silifas,army clothes,face marks…….etc. Shiyawa yayi cikin three quarter blue with white t-shirt,ya daura a gogon diamond na millions of dollars, silifas ya saka masu lashi,sun karawa fararen yatsun kafan shi kyau ,sai mai muce Tabarakallah Masha Allah . Fitowa yayi daga dressing room din,cikin room din ya koma ya zauna ,daukan system nashi kiran iPhone, operating nashi cikin kware wa da Birgewa. Sai lokacin na kare masa kallo ,Masha Allah fari ne tass ,kana ganinsa kaga balaraben mutum,yanada manyan eye bolls (grey color) masu daukan hankali,ga hancinan zuwait kaman pencil,yanada saje daya zagaye dan karamin bakinsa mai shape din heart ❤️ so reddish kaman yasa Jamba ki. Sai dai fuskansa kaman anyi gobara ,dan a hade take tam,danshi baisan meye dariya ba,ga kwarjini dan wannan a jinin sa yake. Shigowa dakin yayi bakinsa da sallama ,amsa wa “BOSS LION “ iya labban bakinsa ,idan kana wajan ma zakayi tunanin bai amsa ba,bayan amsa sallaman dayayi ,bai kalla ko inda yake ba ,yiya yi kaman bai San da halittasa ba. Junaid ne yashigo fiskanshi a sha gwabe hanun shi dauke da coffee ☕️ ,ajiye wa yayi akan bed side drawer yace yaya boss am so sorry 😢 please I will not do its again , please 🙏 tare da kama kunen shi daya yayi kalan tausayi. Zaka tashi ka fita daga dakinan ne ko,kuwa sai nayi ball da Kai ya fada cikin tsawa jijiyoyin kansa sunyi rudu rudu tsabar bacin rai . Fashewa da kuka junaid yayi ,ya mike jikin sa na kerma ya fita daga dakin,a bakin kofa ya samu Ashman “zai shiga ,alamun kuma Yaji abunda yake wakana ,fadawa yayi jikin “Ashman din ya saki kuka mai taba zuciya ,bubbuga bayanshi yake yi alamun rarrashi,amma bai bude bakinsa ba,sai da yaji ya fara sakin Ajiyar zuciya,kafun ya sake sa . Meyasa baka jin magana ne ,janshi yayi suka koma falo ,,amma dai kai ma kasan halin “BOSS LION “ wannan abunda kake ji ba dai dai bane ,kana tunanin bama sanka ne muku hanaka,no,dan kare ka daga shiga fushin ubangiji ne . Zuwa club ba’abu bane mai kyau ,kasan alkawari ya dauka wa ummie kafun rai yayi halinsa,ta damka amnan mun a hanun sa. Kokari yakeyi yaga ya cika amanannan, maza tashi kaje ka wanke fuskan ka ,Zanyi mishi maga na idan ya huce ,tashi junaid yayi ya fita daga side din. Please anayin comment da likes 🙏 2024/2025🔥 Written by Amid✍️ 💋*_ SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌎Destiny,Love ❤️& Romance 💋 Written by Amid✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Paid book ne Free page 📃 7 Bayan tafiyan junaid,Ashman “ ya mike ya shiga dakin “BOSS LION “ yana zaune a inda junaid ya barshi,coffee yake sha hankali kwance ,amma fuskanan kaman anyi mishi mutuwa,zama yayi a gefensa , kasa magana yayi dan yana Jin shakkan yimasa magana ,dan shima yanada nasa laifin. Cikin dake wa da aro jarumta irin tasu ta soldiers “yaya “BOSS” Dan Allah kayi hakuri,insha Allah addu’a zamu na mishi ,indai Muna yi masa addu’a Allah zai karba,idan Muna yawan yi fushi dashi ,yana shiga cikin damuwa ,dayake sa yake kara maida weeds or shisha abokin rayuwan sa. Kamata yayi Muna kwantar masa da hankali dan bashi da kamarmu,please we are so sorry w……………”maganan nasa yatsaya be dalilin wani kallo da “BOSS LION “ ya masa ,ba tare da yayi magana ba ,yanuna masa kofa da ido,dan bai cika yin magana ba ,dan akwai wani SIRRIN DAKE BOYE da ke cikin zuciyansa bayasan ana tuna masa da abunda ya wuce. Tashi yayi salun alun ya fita daga dakin ,almost 9:30am ,bayan fitan “Ash” da minti goma sai gashi ya dawo da Trey a hanun sa ,mai kyau da dauka hankali golden color ne ,ajiye wa yayi akan center table dake cikin dakin. Yakai 10mins a zaune akan king chair dake dakin,kafun “BOSS LION “ ya mike ya zauna a dayan king chair ,tare da yin crossing legs nasa,ba tare da yayi magana ba ,Ashman kam wannan abun bai damesa ba ,saving nashi yayi abinci irin nasu nacan,a hankali ya fara cin abincin ,ci yake yi kaman yana yanga, cikin nutsuwa da Jan aji. Shap shap ya gama cin abincin,tare da mike wa ya shiga toilet dan ya wanke bakin shi ,shikuma Ashman ganin ya shiga toilet sai ya tattare kwanu kan ya fita dasu ,yakuma fesa air freshener masu sanyi dadi. Fitowan da yayi bai ga Ashman ba ,yasan ya fita,koma wa yayi ya zauna a L-shape chair dake gefen center table din da wasu docoments da system. Bai fito ba sai karfe daya shima sallan azahar ne ya fito dashi dan kwata kwata baya wasa da sallah komai yake yi zai bari ne yayi sallah. ________________________________________________📚 Abuja Yau takama Wednesday,tunda ta tashi daga bacci take Jin kwadayin shan ice cream,dan yau cikin farin ciki ta tashi daga bacci. Wanka tayi ta shirya cikin Riga da wandon makarata tareda wani mini hijab tayi Kyau sosai,daukan school back nata tayi ta wuce falo. Falo ta sakko bata samu kowa ba ,wuce wa tayi side in Ammi, akan sallaya ta sameta dan azkar take yi,cikin murmushi ta karaso inda Ammi take “Ammi Ina kwana “lafiya kalau autar Ammi ,kin tashi lafiya”lafiya kalau ,kallanta Ammi tayi tace yau kuma autar Ammi mai muka samu mai dadi naga sai murmushi kike yi , darıya Shukrah tayi tare da cewa wallahi yau kwadayin ice cream nake yi” Toh ai sai kije kisamu alameen ki fada masa kinasan san ice cream din zai kaiki ai. Cikin shagwaba ta turo baki tace “ Ammi amma kinsan halinsa yanzu sai yace bazai kaini ba “karki damu autar Ammi ni zan mishi magana idan ya shigo, cikin Jin dadi shukrah tace thank you best mother in the world,shiya sa nake sanki wallahi” dan dan kwalanta Ammi tayi,tare da cewa tashi ki barmun daki marar kunya kawai ,cikin darıya shukrah tace Ammi ba rashin kunya bace har cikin Raina nake fada,ta karasa magana tare da fita daga dakin tanaji Ammi na ce wa Allah ya kiyaye hanya. A wajen stairs taga alameen zai wuce dakin Ammi ,cikin Shan kamshi tace yaya alameen good morning “morning ya ce tare da haura wa dakin Ammi . Ita kuwa yusrah wuce wa dining tayi ,breakfast tayi cikin sauri ta gama ta fita dan driver yana jiranta , shiga tayi motan driver ya ja motan suka wuce school. A dakin Ammi kuwa yana zuwa yayi knockingna kofan dakin,izinin shiga Ammi ta bashi ,zama yayi a kasa kafun ya fara gaisheta,Ammi Ina kwana kin tashi lafiya, kinsha maganin jiya da daddare,tsaya wa kawai tayi tana ganin sa ,soyayyarsa kullum karuwa take yi a cikin zuciyan ta ,yanda yake kulawa da ita abun ba karamin dadi yake mata ba. Lafiya kalau”Alhamdulillah,maganina kuma nasha dana ci abincin dare saura na safe, Toh Ammi Allah ya Kara sauki”Ameen ya Allah “Ammi akwai abunda kuke buka tane idan na fita na taho miki dashi,” a’a babu komai Allah yayi maka albarka ameen yace tare da tashi zai fita . Cikin sauri tace alameen ,komawa yayi ya zauna ,tare da maida hankalinsa Kanta ,Yauwa dama shukrah ce ta tashi da kwadayin shan ice cream “Toh Ammi baga driver ba sai ya kaita su siyo,”baza’a aika drivern ya siyo ba, kai nake so kai nake so ka kaita inda kake zuwa. Cikin son danne baccin ransa yace Toh Ammi Insha Allah,ya fada tare da mikewa “Toh Allah ya kiyaye ,yayi maka albarka ,Ameen ,tare da fita da ga dakin. Falo yakoma ko zai sameta ,amma batanan tariga da ta tafi. ___________________________________________🌹 7:45pm Idar da sallanta kenan taji ana knocking na kofan dakin ,sai kuma taga ya shigo cikin dakin , ganinsa tayi ,sanye yake cikin maroon yad mai tsada anyi mishi dinkin half jampa,dinkin zamani daidai jikin sa. Cikin takunsa mai dauke da nutsuwa ya isa inda take ,baiyi wata wata ba ya kwade Kanta ,dan har janzu bacin ran bai gama sake shiba. Wato ni kin rainani harda zuwa wajen Ammi kice mata kina kwadayin ice cream, kuma ni kikeso na siya miki ko ,ya kara sa magana tare da Zare mata ido. Cikin gunguni tace nifa ,bace wa nayi tace maka kakaini ba , kawai ce mata nayi Ina kwadayin shan ice cream,sai tace bari kazo zata ce maka ka kaini. Kwafa yayi tare da cewa zaki sanine, wuce kije ki shirya na baki Nan da minti biyu kısa meni a packing space “Toh tace tareda mikewa ,shikuma fita yayi daga dakin. Wani half Sunnah hijab ta dauka yellow color ta daura akan blue jeans and yellow t-shirt din dake jikin ta ,ta fito cikin sauri ta wuce parking space,anan taga maercese benz 350 maroon color yana kawo wuta, wuce wa tayi tare da bude front site zata shiga , tsawa ya daka mata yace wallahi idan baki koma kin saka kayan arzikiba,jikinki sai ya gaya miki,na baki Nan da one minute ki fito. Zum buro baki gama tayi ,tare da konawa dan bata San duka. Komawa tayi ta dauko abaya purple color mai fadin hannu daya sha stones tayi rolling na gyalen tayi kyau sosai, cikin sauri ta wuce packing space,ta bude motan ta shiga ,bai ce mata komai ba har duka Isah hadadden wajan shan ice cream dasu burger 🍔 ,shawarma,pizza,popcorn,drinks ,chocolate,birthday cake,snacks da abubuwa dai kala kala. Shiga sukayi wajen dan babu hayaniya dan wajene na yayan wane da wane suke zuwa irin wajen. Mentioning na abubuwan da take so tayi iri su burger ,popcorn,chocolate ,ice cream take so ,kawo mata akayi a wani bag mai dauke da tambarin shop din. Wuce wa sukayi suka koma cikin mota,kuna motan yayi tare da daukan hanyan gida , bude bakinta tayi tare da cewa yaya alameen Nagode Allah ya saka da alheri , Ameen yace daganan babu Wanda ya sake magana a cikinsu har suka iso gida. A falo suka tarar da Ammi da Abu zaune suna hira,gaishe da abba yayi da yimishi ya office sannan ya koma dining ya zuba abinci kadan,dan kansa ciwo yake masa,bayan ya gama cikin abincin ya dawo falo anan ya tarar da shukrah sai shagwaba take musu sukuma suna biye mata. Sai da safe ya musu tareda wuce wa dakinsa dan ya kwanta. Shukrah kuwa yana ta fiya ta tashi ta kwashe laidodin ta tawuce dasu daki tare da musu sai da safe,dan Ammi ba cin irin abubuwa Nan take yi ba,tana shiga dakinta zama tayi ta bude laidan data shigo dashi ta dakko ice cream in ta saka a fridge,ta fara rage kayan jikin ta ,ta shiga wanka,bayan ta fito ta saka kayan bacci Riga da wando Marasa nauyi milk color. Dauko ice cream din tayi daga fridge da burger ta ,ta zauna a gefen gadon tana sha ice cream in ta kuma tana cin burgern ta ,dan dadi har lumshe ido take yi. Bayan ta gama ci ,ta shiga toilet tayi brush, ta koma daki ta kashe wutan dakin ya saura iya bedside lamp ine ya rage tayi addu’a ta kwanta Asuba tagari 2024/2025🔥 Written by Amid✍️ 💋*_SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌎 Destiny,Love❤️& Romance 💋 Written by Amid ✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Book 1 page 📃 8 _____________________________________________✍️ USA 🇺🇸 Zaune yake a garden ,jikinsa sanye da three quarters da t-shirt armless daya fito da surar jikinsa irin na kar fafan mazannan,gaya sake curly hair sa ,ya kishin gida a man kujera ,garden din yana da girma sosai daya kawatu da red roses ,yellow,pink,purple,blue daya kawata wanjen ga tress of every kind of fruits,apples,banana, oranges, guava,grapes,strawberries etc. Gasu manya manya ,ga wasu outdoor chairs and tables wajen ya hadu iya haduwa. Yau kwanan sa biyu da dawowa,ya karbi document din da yabawa Ashman aiki,ya duba ya gani bai gamaba amma bai ce masa komai dashi saika manta da kamasa lafi tukun zai hunkun taka a bazata zai maka hukunci. Daga can nesa akwai sojojin da suke ta shawagi ,dan suna iya ganinsa daga inda yake zaune. Ashman yazo garden , zama yayi a kujeran dake passing na “boss LION “ sanye yake da wando jeans da red t-shirt. Good morning yaya boss “batare da ya amsa ba ya “meyasa Baka gama abunda na saka kaba”da ga sama yaji wannan tambayan ,jin wannan maganan sai da zuciyansa yansa tabada irin dummm ,dan a bazata yaji maganan harya manta. Jiyowa yayi yakala “Boss lion “ idonsa a lumshe ,zaka rantse bashi yayi maganan ba ,yaya boss am so sorry,nayi kokarin naga nagama aikin amma abun yaci tura,wallahi banso har kadawo ban gama aikin ba” very good this is not a reason that will make me not to punish you, dan bansa abu aki gamamun shi akan lokaci”so I must punish that person. Let go, mikewa Ashman yayi kaman zaiyi kuka yabi bayan “Boss lion “ wani babban fili sukaje, kana ganin wajan kaga wajan horon sojoji, suna tafiya sojoji suna binsu a baya. Abubuwan horo kala kala parts parts, kowani punishment da bangarensa , Waje ne dayasha tiles irin mai santsin nan, zama “boss lion “ yayi a kujera mai kyau yayi resting bayansa da kujeran tare da yin crossing legs,umarni ya bawa sojojin da sutafi , mutum biyu ne suka tsaya,dan suma akwai abunda zasuyi ne. Man abinci suka zuba a wajen tare da fasa Kwai daya wa wajan ,kankace me wajan yayi wani irin santsi da mutum yana ajiye kafansa zai fadi,suna gamawa suka bar gurin, “Remove does trouser and the t-shirt “gyada kai yayi dan babu bakin magana ,cire wa yayi ya saura dagashi sai boxers da vest, “you can move” “boss lion “ ya fada. Okey yace tare da daukan lemon 🍋 akan spoon in , idan lemon ya fadi zai koma farko ne . Taku daya yayi zaiyi na biyu santsi ya ja kafansa ya fadi, saida gwiwan sa ya bugu,amma haka ya tashi ya koma baya,shima a na uku ya fadi ya buga kwankwasan sa ,runtsa idanunsa yayi jin wani zafi ya ziyarce shi. Da kyar ya tashi ya fara ya kusan rabin wajan ya fadi ya sake buga gwiwansa ,sai daya saki karamin Kara, ya kai kusan 30mins yana abu daya ,Duk ya fita hayyacinsa abunku da farin fata,fatan tayi jajir dashi Dan yaji kiwo awaje daya wa . Tafiya yake yi yakusan zuwa karshe wajen baifi yayi taku biyu ba yafita,kafansa ya zame ya bugu akansa dan unexpected ya fadi,sai dayayi kara dan bakaramin buguwa yayi ba , tuni jini ya wanke masa fuska. Karan da ya yine ya janyo hankalin “boss lion “ da yanzu aka turo masa da sako,shiyasa baiga lokacin da Ashman din ya fadi ba . Mikewa yayi yana tafiya cikin takunsa na kasaita da nutsuwa ,dan fusknsa bai nuna komai ba dan a tamke yake kowani lokaci . Sai dai shi har cikin zuciyansa yakejin radadi abunda ya saka ashman din ,dan yana balain son yan uwansa,amma san dayake musu bashi zaisa yaki punishing nashiba a duk lokacin daya so. Yana isa wajan ya samesa har ya suma ,dan ba karamin jini yake zubarwa ba , daukansa yayi chak akan kafadansa,ya fito daga wajan ,anan ya samu sojoji da kuma junaid da uncle tareeq da zuwansu kenan,dan sun zone dan su karbi ATM ,shopping suke son suyi,akan hanyansa na zuwa nanne suka hadu da uncle tareeq suka taho tare. Zuwansu Kenan sukaga halin da Ashman yake ,dake hanun “boss lion” Hankalinsu ya tashi ganin yanda yake zubar da jini ,ba kaman junaid da tuni ya fashe da kuka,sukabi bayan “boss lion” hanyan clinic suka je ,clinic din yana da girma sosai kaman asibiti dan yafi wani asibitin girma ga kayan aiki available. Direct wani babban daki ya shiga da Ashman dakin maikyau kaman ba dakin jinya ba , yana shiga ya rufe kofan dan bayasan kukan junaid ya damesa wajen treatment in. Cikin kware wa da iya aiki ya wanke jinin tare da mishi dressing na wajen ya daure kan da bandage 🤕 ,ya kuma gasa masa jikinsa,yanda idan ya tashi bazai ji wani ciwo sosai ba ,alluran bacci baci ya masa,bazai tashi ba sai nan da 6hrs . (Tun yana karami wannan burin ummie sa ne ya zama likita,shiyasa bayan ya gam karatun likita ya shiga aikin soja ,cikin kankanin lokaci ya tashi yayi tashe kowa yana sansa amma tsoronsa suke ji har president din da Kansa da baya daukan nonsense aiki yake yi bisa adalci dan baya zalunci,abunda yasa ya kara daukaka har yaje matakin da yake yanzu). Fitowa yayi daga dakin ,anan ya samu junaid idonsa sunyi Luhu luhu saboda kukan dayasha bakadan ba, a tsaye suke tareda uncle tareeq da uncle Ibrahim. Cikin sauri junaid ya rungumi “boss lion” tare da sake fashewa da kuka ,bubbuga bayansa “boss lion “ yayi tare da ce masa ,karka damu bawani ciwo sosai bane yaji nanda 6hrs zai tashi kaji. Gyada Kansa junaid yayi cikin gamduwa da maganan yayan nasa, dan baya karya wannan halinsa ne kuma bayanso a masa, shiyasa kuka yarda dashi. Tafiya sukayi tare ,har suka koma parts na su kowa ya wuce dakin sa . ____________________________________________✌️ After some hours ♻️ Zaune “boss lion “ yake a gefen gadon da Ashman yake,tare da junaid, uncle Ibrahim, uncle tareeq, suna zaune suna jiran tashin sa dan time yacika daya kamata ace ya tashi,shikam “boss lion “ bai wuce 5mins da zuwansa ba ,anan ya tarar da su ,suna zaune jiran tashinsa. Bai wuce 5mins ba ya fara motsi da hanun sa alamun zai farka ,cikin sauri junaid ya karaso wajan sa,yayında “boss lion” yake zaune ko alamun motsi bai yiba ,fuskanan a tamke. A hankali ya fara bude idonsa ,dishi dishi yake gani ,sai dai yana iya jiyo maganan su junaid sama sama” yaya Ashman” ka tashi,ya jikin naka, har dasu uncle tareeq da uncle ibrahim suna masa sannu,gefe uncle ibrahim ya koma yana dariya kasa kasa ,a hankali yace hmmmm yaro yaro ne. Rufe idonsa yayi da yakara dark ash , sannan ya sake bude wa, sai a lokacin yake ganisu dake ,daya bayan daya yake ganinsu,kafun yafara kokarin mike ya kasa dan jikin yayi tsami, sai lokacin “boss lion “ ya tashi ya mikar dashi da samasa filo a bayansa. A hankali kaman mai rada yace masa,ya jikin, akwai inda yake masa ciwo ne,cikin sanyi murya yace da sauki ba abunda yake mun ciwo ,kirfin jikinane kawai bai dawo ba, sai kuma ya marairaice tare da ce wa “please “ yaya boss “ am sorry, ba tare da sake ganin Saba yace it’s okey “ya koma ya zauna. Su junaid da suke wajen babu Wanda yansan mai suke cewa, junaid ne ya sake cewa “ yaya Ashman tun dazu nake ta maka magana kaki kulani ya fada cikin ya shagwaba ya bata rai alamun yayi fushi. Murmushi da bai shirya bane Ashman ya subuce masa”haba my little brother ai bama haka da kai ko ,ba mai shiga tsakanin mu sai Allah. Toh ai kaine kaki kulani “ok am sorry,Shikkenan,gyada kai yayi kaman wani yaro . Tashi boss lion yayi ya fita daga dakin ,dan shi yanada abunyi. 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌎 Destiny,Love ❤️ & Romance 💋 Written By AMID ✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Paid book ne Book 1 page 📃 9 ______________________________________________✍️ Gombe Gabukka Yau ta kama asabar zataje islamiya da yamma,shiyasa ta tashi da sassafe tayi duk aikin data sabayi, ko karya wa batayi ba ta tafi . Tafiyan hour daya da tayi ta isa g.r.a ,tana shiga gidan ta samu ba kowa ,kitchen ta wuce dan yin abunda ya kawo ta ,cikin kankanin lokaci tayi yam bolls da ferfesun kifi tare da souce. Dining takai ta jerasu,dan har lokacin babu Wanda ya fito ,masu aikine kawai suke aikinsu , koma wa tayi kitchen daura abincin Rana ,jallof rice with coslow take son yi. Bayan ten 10mins taji maganan mommy tanata masifa” wai Ina yarinyar nan takene batazo tayi saving namu ba,ko so takeyi ni na tashi nayi saving abincin”cikin sauri ta fito daga kitchen din tanufi dining area ,anan ta tarar dukansu suna zaune amma banda Zainab,dan yau weekend ne basa zuwa school. Gaishe dasu tayi cikin sanyi muryanta mai dadin sauraro,amsa wa sukayi amma banda mommy dan ciki ciki ta amsa yanda ba kowa ne zai san ta amsa ba. Saving nasu tayi cikin nutsuwan da a jininta yake ,bayan ta gama zata koma kitchen taji muryan mommy “ki zuba abinci ki kaiwa zainab dan batajin dadi,ta fada hakane saboda idon daddy a waje shiya tayi maganan da ladabi. Toh tace tare da zubawa ta daura akan Trey,ta dauka ta wuce dakin zainab dashi ,knocking tayi amma ba ayi responding back sai data sake wajan sau uku kafun taji ance yes ,shiga tayi bakinta dauke da sallama . (Yan uwa ku kula dayin sallama a duk inda zuaku shiga koda kuwa kasan babu kowa agurin “kuma wajibi ne ka amsa sallama muddin kai musulmi ne dan haka akiya ye a yawaita yin sallama dakuma amsa wa, mun manta da zantukan” annabi Muhammad (s.w.a) yace karami shi zai fatawa babba salama ,Wanda yake kan abun hawa shi zaima Wanda yake tafe sallama “kuma annabi (s.w.a) ya kara da cewa mai rowa shine Wanda baya wa mutane sallama *Assalamu Alaikum [lada 10] *Assalamu alaikum warahmatullah [lada 20] *Assalamu alaikum warahmatullahi wabarkatihu [lada 30] “ Allah ya bamu ikon amfani dashi “ Ameen) A kan gado ta ganta ,garau babu alamun rashin lafiya a tattare da ita , jikinta sanye da kayan bacci ,da kusan komai na jikinta Ana gani, a hakan dan tana da kyau sura. Ajiye Trey tayi akan bed side drawer,ta juya zata tafi ji kawai tayi an fisgo ta , saura kadan ta fadi dan unexpected ne. “Ke wave irin jakace ,ni kike tunanin zan matso da trey din,kuma idan na gama ci ni kikeso na fitar dashi,,dan haka ki tsaya daga can wajan kijirani har sai na gama cin abinci ki fitar da plate din. Ran SULTANA in yayi dubu to ya baci dan ta tsani wulaqanci dan bata dauka, cikin muryan bacin rai ta fara magana “ wallahi ki iya bakin ki , ce miki akayi dan Muna aiki a gidan ku ,shine zai baki daman yi mana abunda kika ga dama ,toh bari kiji “idan bakida hankali ne toh kije ki nemi hankali,dan na tabbatar harda duhun jahilci ke damun ki, da rashin sanin darajan dan adam ,Allah daya halicce ki shiya halicce mu, bawai dan yafi sanku bane yayi ku masu kudi,ba kuma dan baya San mu bane yayi mu talakawa ,dan haka kishiga hankalin ki ,idan ba haka zan iya miki abunda bazaki ji dadi ba. Zainab kam tsaya wa tayi tana gani ta ,sai kuma ta kwashe da dariya” hmmm Lallai biri yay kama da mutum,dama nasan badan Allah kike yi shiru ba ,kinayi Abu sum sum irin na Muna fukai masu fuska biyu,har kınada bakin ce mun jahila ,kinsa ba’a jahila daya sai biyu k………….” Cikin sauri SULTANA ta ce “Karki kuskura ki karasa dan ranki zai baci ne ,dan haka kowa ya tsaya a matsayin sa ,koda wasa karki shiga harkana , abinci kuma indai nizan ajiye miki toh zaki mutu baki ci ba ,trey ma in kinga dama kibarsa a dakin har duniya ta nade “tsaki ta ja tare da fita daga dakin. Zainab kam baki bude abi bayata da kallo tare Dayi kwafa tana ayyana abu a ranta. Kitchen ta koma dan duba girkin data daura ,zuwa biyu da rabi ta koma gida ,shima keke nafep tahau,idan tace zata tafi da kafa zata makara ne. Bayan dawowanta gida bata samu kowa ba ,harda innah”adda deeje kawai ta samu a gidan itama fita zatayi dan kicibuss sukayi a bakin kofa zata fita,sai hararanta takeyi. Cikin sauri ta shirya cikin blue and white uniform din ,blue wando da Riga sai hijab har kasa, tana gamawa tarife gidan takai key makwabtansu ,wuce wa islamiya tayi dan bashida nisa da gidansu,tana isa ta wuce ajinsu ,dan kowa ya zo dan kullum itace mai zuwa latti,zama tayi gefen wata yarinya ,zasuyi sa’anni da ita black beauty abunta. Yarinyar gefeta tace”ke kam da zuwa latti yana tabo,toda yayi miki,kullum sai kinzo latti “kedai Bari bada san Raina nakeyin lattin nan ba kaw……..”maganan ya tsaya ne ganin mala minsu ya shigo class,tilawa suka farayi kafun ya fara karban hadda ,har ajazo Kanta ,cikin nutsuwa da muryanta mai dadi ya fara bada hadda kowani harafi hakkinsa na tajweed,har ta gama ba’a cita gyara ko daya ba,dan Allah yayi mata brain na daukan abu da wuri. Sai 5:30pm aka tashe su ,kowa ya kama hanyan gida ,tare da asmau suke tafiya suna hira jifa jifa,kafun zuka rabu asmau ta shiga gida takuma ta cigaba da tafiya harta isa gida. Tana dawo wa ta samu har yanzu basu dawo ba ,sai tashiga makwaftan ta karbo kin abude gida tashiga .daki tashiga ta cire kayanta ta daura zani,tawuce bandaki tayi wanka ta canja kaya zuwa material. Girki ta daura ,bata gama ba sai bayan magrib ta gama ,a lokacin an fara kiraye kirayen sallan isah,tana cikin sallah taji haya niyansu alamun sun dawo . alqur’ani tafito dashi tana koyan haddan da aka basu,tana gama ta kwanta dan har yanzu babu Wanda yashigo dakin dan indai suka zo da abun dadi ,a dakin innah suke tsayawa su cinye”cikin kankanin lokaci bacci yayi awun gaba da ita. 🔥 sai mun hadu gobe idan Allah ya kaimu❤️ 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌎 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 Written by AMID ✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Book 1 page 📃 10 _______________________________________________💞 Abuja , Nigeria 🇳🇬 7:30am Zaune take akan dining tana breakfast,sauri takeyi dan yau zasu fara exams,bataso tayi late. Tana gama cin abincin ta tashi zata fita taji muryan Ammi “ autar Ammi tafiya ne babu sallama “yi hakuri Ammi bana so nayi late ne”Toh Allah ya kiyaye ya bada sa’a” Ameen ta amsa tare da ficewa daga falon. Bayan kaman minute biyar 5 sai gata ta dawo ,Ammi da to wanta Kenan daga kitchen tace “ ah ah autar Ammi meya faru naga kin dawo ko kinyi mantuwa ne. Girgiza kai tayi cikin shagwaba har idanta ya fara kawo ruwa tace “Ammi musa driver ne bashida lafiya wai baizo ba yau gashi nakusa yin latti” sai kije ki samu yayan naki ki fada masa idan yaso sai ya kaiki,Toh tace tare da wuce wa dakinsa ko sallama batayi ba tashiga dakin. Shikuwa alameen bai Nima da fitowa daga toilet ba da towel a kugunsa yana kokarin saka kaya kawai ya ga mutum daga sama babu sallama bare excuse. Cikin tsawa yace”wai ke wace irin marar hankali ce da kishigo dakin mutum ba sallama “Anya shukrah kina fahimtan abunda ake koya miki kuwa kodai kawai barnan kudi akeyi a banza da har yanzu bakya gane abu mai kyau da mara kyau”zaki wuce ki fita daga dakin nanne ko sai ba balla ki. Cikin sauri ta fita daga dakin ta sharar kalla ,komawa tayi main falo ta zauna a gefen Ammi “auta mai ya faru naga kin fito kina sharar kwalla,”babu komai Ammi ,kafana na bige a jikin gini,yaya ma cewa yayi na jirashi a falo yana zuwa”Toh sai kijirashi danni daki zanje na kwanta ,tashi Ammi tayi ta wuce dakin ta falon ya saura yusrah kadai. Zaman 6mins tayi sai gashi ya fito,jikinsa sanye da dark blue yad daya amshi jikinsa ,dinkin zamani aka yi masa , key ne a hanun sa dan musa driver jiya yace masa bazai samu zuwa ba bayajin dadi ,shiyasa ya tashi yayi wanka dan yazo ya kaita. Hanyan fita yayi ,batare daya ce mata komai ba ,shukrah ganin bai kula taba yasa ta tashi tabi bayansa ,packing space ta nufa , anan ta gansa a cikin BMW white color, bude wa tayi tashiga tare da cewa yaya alameen Ina kwana,Dan Allah yaya kayi hakuri mantawa nayi ne shiyasa”lafiya , nangaba ko bani ba karki sake shiga dakin mutum ba tare da kinyi sallama ba ,babu kyau kiji ba , sai ki gyara “ Toh tace. Har suka isa ba Wanda sake cewa komai, zata fita yaba ta pocket money tare da cewa “ kiyi karatu banda wasa fah uhmmm tace tare da yi masa godiya ta karba kudi tasaka a pocket nata . Tashiga school shikuma ya juya motan ya koma gida . _______________________________________________✍️ USA 🇺🇸 Yau kwana uku Ashman yana jinyan jikinsa ,kuma Alhamdulillah jikin nasa yayi sauki sai abunda ba’a rasaba dan kullum sai “boss lion “sai yazo yayi masa treatment din wajan ,dan yanzu baya clinic ya koma dakinsa sai dai baya zuwa office ya rubuta letter a ogansa wato “boss lion “ a kan bashida lafiya,dan haka tsarin aikin yake. “Boss lion “ Kwance yake akan gadonsa,jikinsa rufe da bargo,amma bai rufe kansa ba iya kafa da. Motsi ya fara alamun zai tashi ,bakinsa dauke da addu’an tashi daga bacci . (Alhamdu lillahil-lathee ahyaanaaa ba’da maa’amaaatanaa wa’ilayhin nurshoor). Bude idanun sa yayi da sukayi grey color sai shining sukeyi kaman ba yanzu ya tashi daga bacci ba ,mikewa yayi ya sauko da kyawawan kafafunsa farare tass ,ya mike ya shiga toilet. Fito wa yayi daure da towel a kugunsa ,wucewa yayi wajen dress mirror ya sha mai dasu lotions,kafun ya wuce dressing room ,after some minutes sai gashi ya fito sanye da kakinsu na sojoji ,tubarkallah Masha Allah,Allah yayi baiwan kyau anan ,ya fito a balaraben sa ,ga curly hair nsa daya sha gyara ,Moses nashi dukda yana cikin riga zaka shaida kakkarfa ne bana wasa ba. Sai kamshi theatre yake masu masifan kamshi dake sa nutsuwa da kuma tafiya da zuciya mace ko namiji. Cikin Tafiyan kasaita irin na ingarman namiji main falo,sojojin dake falon sai Sara masa suke yi ,jikinsu har kerma yakeyi wajen ganin basu ji kuskure ba , fito wa yayi cikin gidan anan ma sai kamewa sukeyi suna sara masa ,kaman zasu masa sujjada,ko kulasu bai yiba kaman baisan sunayi ba. Wajan wasu jahilan motoci ya nufa na millions of dollars kusan goma sha biyu ,shadaya 11 bakake ne masu tinted sai na tsakiyan BMW 7 series,bude masa james yayi tare da Sara masa. A tare convoys din suke gudu kaman zasu tashi sama,direct head quarter suka wuce a jere abun gwanin sha’awa . Sunkai 10mins da tsaya wa kafun aka bude masa ya fito,fitowa yayi fuskanan a murtuke ta cikin face marks din dake fuskansa. Head quarter ne babba anan office na jiga jiga sojoji suke ,ga sojoji ta ko Ina suna yawo,upstairs 10 ne gashi na glass ne daya kawata wajan. Suna shiga ciki sojojin sai mekewa sukeyi suna sara masa tare da kame wa,direct wajan lifter yaje shida james dake rike da document bashi a hannu,suna shiga james ya danna 10 wato na karshe kenan ,within seconds lifter ya bude ,fitowa sukayi suka tsaya a bakin wani kofa mai kyau ,ta saman an rubuta “FIELD MARSHAL office “. James ne ya bude kofan ,”boss lion ne ya fara shiga kafun james ya biyosa da document din ya ajiye akan table din tare da Sara masa ya juya ya fita. Office ne mai girma sosai daya kawatu da ababen more rayuwa,komai white color ne a office din,ga sanyi ac da kamshi ne kawai ke tashi a office din, a cikin office din akwai falon a cike shima komai white and golden ne sai resting room shima yanada girma sosai mai dauke da furnitures masu kyau da tsada. 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌎 Destiny,Love ❤️ & Romance 💋 Written by AMID ✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Paid book ne Book 1 page 📃 11 Zama yayi akan kujeran table din ,tare da bude system ya fara aiki cikin kware wa da basirah ,aikin yakeyi cikin nutsuwa . So yake yi ya gama aikin daya rage masa dan yana so yaje Spain gobe yayi kwana daya ya dawo,shima gayyatan sa akayi . 3:50pm ya fito daga office din suka koma gida . Wanka yayi ya shiya cikin black jeans and black t-shirt,p-cap ,face marks,booth ,watch,Duk komai black colour ne ,kafun ya daura black jacket akai ,idan ka gansa akan hanya ma ba lallai ka ganesa ba . 3 floor ya nufa, direct dakin Ashman ya nufa ,ya samesa zaune yana duba wasu files. Ashman zake zaune kamshin turaren “Boss lion” ne ya ankarar da shi da zuwansa, nufan inda yake “Boss lion “ yayi tare da tambayansa “ how are you? And your body ,I hope your felling good 😌 da kyar ya karasa maganan tsabar miskilancin. “Good afternoon yaya”am felling ok,Alhamdulillah “ zanyi tafiyane kuma na sirri nakeson yi ,dan haka kakula da kanka da kuma junaid cewan “Boss lion “ . Hugging nasa Ashman yayi tare da sakar masa Kiss a gefen kumatunsa ,shima maida masa yayi tare da juya wa zai tafi yace muryan Ashman “safe trip yaya”. Bai kula saba yayi ta tafiyansa, cikin wani Boyayyen hanya yabi ya fuddashi daga gidan batare da kowa ya gansa ba ,anan ya tarar da james a cikin mota,cikin sauri James ya fito ya bude masa kofan ya shiga sai airport, yana isa private jet nashi ya shiga ,shigansa within 6 minutes jet din ya daga. (Allah ya kiyaye boss lion) ________________________________________________🙏 Gombe , Nigeria 🇳🇬 Tana tashi da Asuba tayi sallah,ta zauna bitan karatun qurani kafun ya fito dan yin aikin da ta saba ,tana cikin wanke wanke taji muryan innah na ce mata” garbati jiya ya kawo kudin auren ki ,kuma ansa nan da sati daya zaki tafi dakin mijin ki dan ninagaji fenada kujecan Ku karata ,a tsiya ce” Cikin shega adda Habiba da adda deeje suka tafa,yau sun tashi da wuri wata kila akwai abunda zasuyi ne. Adda Habiba tace” ah ah SULTANA anyi goshi ,haka kawai sai kiyi wuff da bawan Allah, adda deeja tace “ basai zai iya zama da ita ba ,dan wannan daga gani ko sati baza AYI da auren ba zata dawo bazawara dan nasan shima ba iya zama zayyi da ita ba “ Cikin sauri innah tace”Ina zata dawo ai wallahi ta tafi ta tafi Kenan ,ba zancen dawowa sai dai tashiga duniya ,yan duniya suganta ,idan ya so sai su kwashi ragowan garbati . Cikin dariya adda Habiba tace “ a kwai shagali har walimah sai mun yi idan ya bar mana gidannan muma mu huta da fitinah . Wasu hawaye masu zafi da na bakin ciki suka zubowa SULTANA , tayi saurin sha rewa ta dau alwashin ko zata rasa ranta ne bazata taba bari ayi aurenta da garanti ba . Tana gama wanke wanken tayi wanka tashiga cikin riga da skirt na atampah yayi nata kyau ,sauri tayi ta gama dan yau har tayi latti ma. Sauri tayi ta fita daga gidan ko sallama bata musu ba ta tafi. Sauri takeyi sanye da maroon color hijab tareda niqab,blue eyes nata kawai zaka iya gani a jikinta, tana isa tashiga tafara aikinta har sukaci abincin safe ,tagama zuwa 2 na rana ta shirya ta fita daga falon,kicibuss sukayi da jabir a bakin kofa . Ko kulasa bata yiba,zata wuce ta gefe kawai ya sha gabanta tareda Mika mata key “ga kinnan ki kaimun abincin Rana dakina,SULTANA kam kallon baka da hankali take masa,magana ya farayi cikin serious yace” abinci zaki Kai mun fah ,Kona taba aikenki dakinane yimun wani abun “ni bazan kai ba kabani hanyan na wuce tun Muna mutunta juna “ please kikai mun daki ni’ina garden da abokina ,idan muka gama abunda mukeyi zai ci abincin ne. “ toh bani key na kai dan kana batamun lokaci ne “mika mata key yayi tare da juyawa ya nufi garden, SULTANA kam komawa tayi kitche ta zuba abinci a plate ya daura akan Trey ,ta dakko ruwan sanyi da Coca Cola a fridge ya daura akan tare da cup agefen. Tana fita daga part din ya wuce boys quaters din, shiga tayi falone mai dan girma daya kawatu da furniture brown sai kofa biyu Wanda daya zai sadaka da dakin jabir daya kuma Na khalifa,gefen dama shine na khalifa na hagu kuma na jabir na hagun ta nufa tare da sa ki ta bude kofan. Tana shiga warin sugari da na shisha ya bugesa alamun ba’a dade da shaba sai da ta toshe hancinta dukda akwai niqab a fuskanta amma ta Tosha hancı ta kafun ta karasa cikin dakin ,dakin Duk a warga je kaman ba mutum ne yake rayuwa a ciki ba. Komai a war gaje towel a kasa kayan da ya cire ma akasa ya wullar ga uban kwanuka a cikin dakin ya kasa fitar wa sai tashi suke yi,a jiye Trey tayi akan table din dake ajiye a tsakinyan dakin ,”kaman daga sama tayi an murda key a kofan dakin ,cikin sauri ta juyo ta duba ,jabir ne tsaye daga shi sai boxers ,tun a falo ya cire kayan ,dariya yayi” yau hakata ta cimma ruwa ,saina dandana zumanki na kauda kwadayina akanki,kullum kina zuwa Ina ganin kayan alatu a jikin ki amma ba daman tabawa ,Toh yaude ga dama ta samu sai yanda nayi dake,ya karasa maganan tare da yin dariya irin na yau kashinki ya bushe. Wallahi idan tace bata tsorata ba karya takeyi amma sai ta dake tace” saboda bakada hankali jahilci yayi maka katutu aka kaida wancan kanwar taka ,zaka wani zo ka yaudareni da cewa na kawo maka abinci . “Bukatar kadai insha Allah,Allah bazai Baka iko ba,wuce wa tayi ta nufi hanyan fita taji ya janyo hijabinta ya cire mata dan karfin mace dana miji ba daya ba . Kokawa suka farayi ,har yayi nasar wullata kan gado,yana kokarin hayewa kanta b…… ( koya zata kaya tsakanin jabir da sultana sai mun hadu ranan monday 2024/2024🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE_*❤ ️( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌎 Destiny,love ❤️‍🔥& Romance 💋 Written by AMID ✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Paid book ne page 📃 12 Kokawa suka farayi,har yayi nasaran wullata kan gado ,yana kokarin haye wa kanta ,batayi wata wata ba ta dauki lamp dake kan bedside drawer ta kwada masa da’iya karfin da Allah ya bata. Ai kuwa tana buga masa ya saki ihu yana tangal tangal jini har ya wake masa fuska ,sai ya fadi kasa sumamme. Cikin sauri ta fita daga dakin da gudu tana sharar kwalla” zuciyanta zafi yake mata abun sun hadu sun mata yawa ,gidan ba dadi wajen aikin ma ba dadi ,har ta fito tsakar gidan bata sani ba,abunda yafi bata ma rai ma”kawai dan nanne wajan samun abincin ta zai yi kokarin ganin ya keta mata haddi”ji tayi ta buge mutum cikin sauri ta daga idonta danganin waje ne ,Ajiyar zuciya tayi ganin Aneesa ce “kiyi hakuri ban ganki bane ta fada tare da cigaba da tafiya. Kamo hanun ta Aneesa tayi dan Allah kiyi hakuri ki dan biyoni ,gyada kai kawai sultana tayi,komawa sukayi falon ba kowa,wuce wa tayi da ita dakinta ,zama tayi a gefen gadon ,daga niqab din Aneesa tayi ta tsaya tana ganin kyakyawan fuskan SULTANA da yayi jajir saboda kukan da tayi. Dafata Aneesa tayi “kiyi hakuri Duk da bansan meya faru ba naga kina kuka,kar kice na miki shishigi amma harga Allah amma harga banason abunda yan gidan nan suke miki ,kawai dai banida yanda zanyi ne,gashi baki bani daman da zan Ina miki magana ba ,ni kuma banason abunda zai kawo sabani a tsakanin mu . Cikin sanyi murya mai hade sanyi jiki tace”babu komai kawai dai ina tunanin abunda ya farune kafun nabar gida ,idan natuna nakan kukan yazo mun ba tare da na shirya ba. Cikin tausayawa Aneesa tace “kiyi hakuri ,komai dan hakuri ,wata rana zakici moriyan sa. Jinjina kai SULTANA tayi cikin gamsuwa da maganan ta ce “insha Allah “,dan Allah SULTANA karki ce na dameki “can we become friends with you please,cikin murmushi daya subuce wa SULTANA tace “why not “dan Koba komai zata na samun sauki ta wajanta. Cikin jindadi aneesa tace yau dai buri na yacika mun zama kawaye,murmushi kawai SULTANA tayi batare da tace komai ba, tana mamakin yanda taga Aneesa take sonta abun ta faranta mata rai . Mikewa SULTANA tayi tace “nagode da kulawan ki a gareni ,zan tafi gida sai gobe “mikewa Aneesa ma tayi”toh bari na raka ki ,sultana tace ai da kin barshi ma basai ki wahalar da kanki ba”a’a ai ninace zan rakaki muje kawai,fitowa sukayi daga dakin,falon kasa ba kowa sai masu aiki dake goge goge. Da kata tayi har bakin get din,sukayi sallama ta koma gida. SULTANA bayan ta koma gida time ya kure na islamiya dan yanzu pass 3 kuma 3 suke shiga class .tana koma wa wanka tayi kawai ta kwanta dan Kanta ciwo yake mata sosai. ________________________________________________✍️ USA 🇺🇸 Harvard university, Junaid ne zaune a cafeteria gama cin abincin sa kenan ya ga body guards Nashi dake kula da duk wani motsinsa koda yaushe suka shigo cafeteria. Fuskansu duk da face marks ,ba lallai a iya gane suba “umarni daga “boss lion” cewa mu maida ka gida yanason ganin ka. Cikin mamakin daya gagara boyuwa a fukansa yace”shi “BOSS LION “din ne yace muku kudauko ni ban gama lectures ina ba”how can that be possible,”brother amma dai kasan bama iya tsallake umarnin “boss lion “ko, daya daga cikinsu ya fada cikin rarrashi,dan in basu rarashe saba akwai matsala. Maganan zuci junaid yake yi” wata kila wani abun yakeson ya fada mada masa” kai No “boss lion” bazai sa a dauko ni saboda wannan dalilin ba,to kodai wani abun ne yasamu ya Ashman ,,tuna hakan yasa hankalinshi ya tashi dan yasan shine bashida cikekken lafiya . “Ok let’s go,junaid yace yayi gaba suka bisa a baya ,daya daga cikinsu ya bude masa kofa yashiga biyu kuma suka zauna a gaba sai wani motan a bayansu, suna fita yaga sun dauki wani hanya daban da inda zasu je. Cikin dan bacin rai junaid yace”wannan wani irin haukane zaku wani canja hanya bayan kunsan so nake na ganin a gida dan nasan meke faru wada ya Ashman ,dan shi zuciyanta tafi amminta da wata kila wani abune ya faru dashi . Tsawa daya daga cikin motan yayi “kai ka shiga hankalinka ,kuma ka iya bakinka,dan kai karamin kwaro ne ,da yayanka zamuyi bada kai ba”so shut up your mouth and keep quiet 🤫 “. Tunda suka yi mishi tsawa ya gane tabbass ba body guards nashi bane sai yanzu daya lura da kyau ya gane dan muryansu ma ba daya bane da irin na sojojin can”zuciyansa buga wa yake yi da sauri sauri ,sai kuma wani tunani ya fado masa “cewa duk inda zasu kaishi yasan “boss lion “bazai taba barin wani abu ya samu junior saba,da wannan tunanin yaji qwarin gwiwan yin magana. “Taya zaku sace ni kuma kuce bazan yi magana ba ‘nasan duk inda zaku kaini a fadin duniyan nan sai “boss lion ya nemo ni cikin some minutes idan zai iya bar……., maganan ya tsaya ne saka Makon powder da suka shaka masa a hanci dan sunga alamun shima yaro zubinsa irin na”boss lion” ne basu da tsoro, gashi ance karsu yarda su taba shi.ga samu ga rashi . (Ni kam nace Hmmmm shima yasan meya takane shiyasa yake fadan abunda yaga dama). Tunda suka shaka masa powder a hanci,a take ya suma a wajan,daganan bai sake sanin inda Kansa ya ke ba dan yariga da ya suma,kuma suma kanin mutuwa ne. (Toh fans dina,ina miko sakon gaisuwa gare ku) SHIN INA ZA’A KAI JUNAID Namu WAYE kEDA SA HANU WAJA DAUKE JUNAID SHIN “BOSS LION “ ZAI ZO KUWA KAMAN YANDA JUNAID YAKE TUNANI,DAN KUNSAN DAI BAYA MA KASAR GABA DAYA. kUNA GANIN JABIR ZAIBAR SULTANA TABUGE SA A BANZA YA ZA’AYI SULTANA TA HADU DA MAI SANTA SHIN BOSS LION ZAI RAGE FUSHI DA ZAFIN RAI, DAURE FUSKA AKWAI WACCE ZATA IYA ZAMA DASHI KUMA BAYA SON GANIN MACE KWATA KWATA WANI SIRRI NE DAKE BOYE DA BOSS LION BAYA SAN TUNA WA ( Ku biyoni a cikin wannan littafin zaku samu dukkan amsoshin da kuke bu ka ta dan ko kwata ba munyi ba a cikin wannan labarin,soyayya ,cin amana,kiyayya,karku bari abaku labari Ina godiya masoya na) Wannan littafin na kudi ne 300 ne bayawa game bukatan karanta complete ga wannan account number 7068845514 opay Fatima mala umar zaka iya turo sha idar biya ta wannan number 08161857656 na gode. 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ (. The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 Written by AMID ✍️ 2024/2025🔥 Bismillah Rahmani Raheem Paid book ne page 📃 13 Bude idanunsa ya farayi a hankali har ya bude su Akan wani dake zaune a kan kujera yayi crossing legs nashi,bakin fata ne ashida haske bakine sosai, ba wani mummuna bane ,Ashekaru bazai wuce 50 ba, amma idan kagansa zakayi tunanin 60 year dan yanada tsufan jiki da wuri. Ga wasu bakkaken kaya ajinkinsu, baka iya ganin fuskansu sun rufe da bakin kalle ,hanunsu rike da gun manya. Junaid yana zaune Akan kujera an daure sa da igiya , darıya mutumin yayi tare da cewa kanin boss ya akayi ne, “gabriel since masa igiyan ,wanda aka Kira da Gabriel ne yaje gaban junaid ya fara sunce masa igiyan dake daure a jikin junaid din yayi tare da dauko masa abinci , mai rai da lafiya ya mika wa junaid yace karbi kaci kar ace mun kashe ka da yunwa dan mu bada kai zamuyi game in ba da yayanka zamuyi ,dan haka kaci abincin ka bamai maka komai muddin yayanka yazo amma idan be zoba kaima kasan sauran,yana karasa magana ya bar wajan . Wanda aka Kira da gabriel kam yana tsaye a dakin yana jiransa, junaid kam kallo daya yayima abincin bai kara yiba dan yanaci,yasan sai an kwantar dashi a asibiti ,koma ya yayi baya ya jinginu da jikin kujeran tare da lumshe idanun sa ,skin nasa har yayi ja . AFTER SOME HOURS ⏱️ Ganin lokaci ya ja ba “boss lion “ ba alamunsa , yasa Gabriel yace” boss benjamin let just finish him ,dan “boss lion ba zuwa zai yi ba ,kaga wanda mu kashe kanin nasa kowa ma ya huta,dan ba karamin son kaninsu sukeyi ba duk da dai har yau bansan ko sune logon saba ko sabanin hakan, idan yaso sai mu tura masa da gawan as a surprise ya fada tare da kwashe wa da dariyan mugunta . Wanda aka Kira da Benjamin yayi dariya tare da cewa” gaskiya Gabriel kanka yana ja shiyasa kaga nafi mu’a mala dakai fiye da kowa ,kaga tunda bai zuba kawai mu tura masa death body of his brother,kaga ko banza munci riba ba zamuyi biyu babu ba ,ba tsuntsu basu ga tarke Junaid kam ya girgiza dajin cewa zasu kashe shi ,dan duk mai rai bazai so ya mutu ba, amma duk da haka bai sare ba ,ya nata addu’an Neman Dauki daga wajen ubangijin sammai da kassai. Benjamin in ne da Kansa ya dauki gun tare da yin huking na gun nasa, ya matso kusa da junaid yace” junaid or what they call u , yau zaka wuce barzaku,dan yayanka ya gagara zuwa karbanka dan haka kashe ka zamuyi . Daganan ya kai gun in kan junaid da niyar harbinsa. Yayinda junaid yake salati dan ya sadakar mutuwa zaiyi tare da rufe idansa gam gam yana jiran saukan bullet. Benjamin yana niyan harbisa kawai sukaji ruwan bullet ta ko Ina a jikinsu dan yan ta’addan sunkai kusan su 100 zagaye da wajan ,within 10minute suka kashe kowa da kowa saura kawai Benjamin,Gabriel da wani dan uwansu daya suka rage basu kashe ba. “Benjamin dake tsaye ya rasa inda zai saka ransa sai zufa yake hadawa kaman yanzu ya fito daga wanka ,dan jikinsa har karkarwa yake yi tsaban tsoro dan fah shi yasan ba komai bane dama kawai burgane yake damun sa da hassada yasa shi dauke junaid in,ji yake yi dazai samu gun daya harbe kansa dan wallahi da punishment in “boss lion” wanda ka kashe kanka kawai ka huta dan bayayin da sauki bare shi da yayi yunkurin kashe masa Kanin sa hmmm. A hankali yake takunsa irin na ingarman namiji mai ji da kyau,kudi,illimi,wajewa,miskilanci ,fuskan nan a daure tamau amma haka bai sa kyawunsa ,kwarjinin fitowa ba jikinsa sanye da jeans with white t-shirt Ya daura black jacket akai masu tsada fuskansa dauke da face mask girar nan a hade fuka kaman zaiyi aman wuta 🔥, bayansa Ashman ne shima jikinsa sanye da da jeans blue da white t- shirts masu kyau sun amshe shi sosai ,shima fuskansa a daure dan shima ranshi ba karamin baci yayi ba . Shigo wa cikin incomplete building in suka karasa yi ,cikin sauri wani soja ya dauko masa kujera mai kyau ya zauna tare da yi crossing na legs nashi . Gabriel kam tunda yayi ido biyu da “boss lion” ya sake fitsari a wandonsa a hakan ma bai San yayi fitsarin ba tsabar firgita da yayi . Benjamin kam tunda yaga “boss lion” yaji kansa ya fara juyawa saboda firgitan da yayi dan shikam yariga da yasani wata mutuwansa ya kama,ya tsokano abunda yafi karfinsa ,dan zufan da yake yi yanzu ya nunka na da ninkin ba ninkin . Junaid kam yana ganin boss lion ya fada jikinsa tare da sakin kuka mai tsuma zuciya tare da cewa “ yaya boss nasani bazaka taba barin wani ya cutar da junior ka ba & I so much love you ,ya karasa magana tare da goge hawayen sa ya dago yana kallan boss lion da ganin sa kawai ya keyi amma bai ce komai ba danshi fah ba iya lallashi yayi ba. Ashman ne yace “Lallai junaid wato kaga yayanka shine ka manta da dayan yayan naka ko, duk na damu amma ka wani shareni kaman badan kai nazo wajan ba ya karasa maganan tare da kara daure fuskan sa. Junaid bai San lokacin da dariya ya kwace masa ba dan yaji abokin fadansa ya fara complain,sauka daga jikin “boss lion” yayi tare da zuwa ya rungume Ashman yace yaya ash kasan ai bazan manta da kai bako ya fada har yanzu da murmushi akan fuskan sa. Ashman dake kallon sa cike da soyayya yace na hakura badan halinka ba ,dan in zance dan halinka ne kam ai inaga bazan kara maka magana ba ,amma ya zanyi inason dan kanina,cikin jindadi junaid yace “ Nima Ina sonka yayan junaid ya fada yana dariya. Mikewa “boss lion “ yayi ba tare da yace wa kowa komai ba ya fita daga wajan Ashman da junaid na suka bi bayansa. Yayinda sojojin suka kama Benjamin,Gabriel tareda dan uwansu mutum daya da ba’a kashe ba aka saka su a gaba har cikin mota , yayinda “boss lion” sun rigada dunshiga cikin nasu dankara dankaran motocin bakake masu tinted suka fita da gudu kaman zasu tashi sama ,tafiyan 30min sukayi suka isa gidan saboda gudun da sukeyi. Bayan sun isama ma sai da “boss lion “ ya ja musu aji kafun ya fito cikin kasaita da nutsuwa ya shiga cikin part in. Bayan sun iso gida ne aka kada kan su ,Benjamin,Gabriel da dayan aka wuce dasu disipline room kuma dakin duhu ,aka rufe su. Junaid da Ashman sun rigashi shiga har junaid yake tambayansa”yaya ash ya akayi kuka gane inda nake . Anan Ashman ya bashi labarin abunda ya faru WAYWAYE ADON TAFIYA ❄️ 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny, Love ❤️ & Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ,game bukatan karanta wa ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar zaki iya turo katin shaidan ki ta wannnan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 14 “ BOSS LION” Zaune yake akan L-shape chair dake dakinsa ,da table na glass a ciki za kaga fishies 🐟 suna yawo da ruwa a ciki saman table in kuma a Kwai wasu roses 🌹 masu kyau each color a kwai ,idonsa a lumshe zakayi tunanin bacci yake yi,ga Ashman dake tsaye a gabansa ya rasa meke masa dadi,kan ganinsa kasan hankalinsa ba’a kwance yake ba,sai murza goshinsa yake yi. Bai dade da dakko “boss lion “ a airport dan bazai dan bazai wuce 20mins ba suka samu sako daga sojojinsu dake biye dashi a baya, sojojin su kasu kashi biyu ne daya suna binsa a matsayi bodyguards nashi daya kuma suna lura da yanda wayancan suke nasu aikin dan “boss lion” ne ya zuba su saboda tsaro. Cewa sukayi sojojin da suke kulada junaid fah duk an samesu a sume ,alamun wani abun suka shaka musu batareda sun ankara ba,gashi basuga junaid ba. Cikin sanyi murya Ashman yace “ kuma duk wanda ya shakawa sojojin mu powder suka dauke junaid, tunda ya fara maganan “boss lion” baice masa Uhmmm ko uhuhm ba idonsa a lumshe har lokacin bai bude idonsa ba. Abunda ya bawa Ashman mamaki shine yanda yaga boss lion yayi mishi banza kaman bai san yanayi ba dan ko ajikinsa mai nuna ya damu da abunda da Ashman ya fada ba dan shifa har cikin zuciyansa wannnan ba damuwansa bane. Ganin bai kula saba yasa ya kara cewa yaya boss junior din kane fah ,da kakeso kuma kake basa kulawa da duk wani tsaro daya kamata,kuma baka barmu munyi kukan maraici ba karkasa niyanzu na fara,ka sanima ko yanzu junaid din kuka yake yi. Ashman fa shi a dole dadin baki yake masa saboda ya damesa,idan ya damesa ko bayaso zai amsa masa saboda ya rabu dashi. Kaman yanda Ashman yake Tunani kuwa hake da ba karamin damunsa yayi ba ko hutawa bai yi ba yazo ya tasa shi gaba da magana kaman zai cinye sa, bude lumsassun idon sa yayi da sukayi gray sosai da alamun gajiya a cikinsu ya bude labbansa a hankali yace” Ashman what going on , just relax, kasamu waje ka zauna kazı kawani tsayamun kerere a kai kaman na maka sata”ko Baka yarda da yayanka naka bane ,kai ma kasan wannan abun yayi kadan ya daga mun hankalina,dan baba tunnanin a duniya nan akwai abunda zai daga mun hankali,cikin fahimta yace “ nayarda dakai yayana. Bayan 2 minute “boss lion” ya cewa Ashman “ miko mun system ina”toh ashman ya fada tare da wuce wa bed side drawer ya dauko ya ajiye masa a gaban sa akan table din gabansa ,bude wa yayi yashiga wasu wajaje yace” matso kaga ni,ba musu ashman ya matso yana kallon system din. Abunda ya bashi mamaki shine yaga duk conversation din junaid da yan daban a cafeteria suka sace shi harda yanda yayi gaba suka bi bayansa , “ boss lion” yana sauka a kasan a ka turo masa wannan video. Cikin yana yin damuwa Ashman yace” to ai bamusan inda suka kaisa ba”karka damu ,I will found it ,as soon as possible, indai har diamond watch in nan yana hanun sa ba abunda zai hanani gane inda yake,cikin mamaki Ashman yace which watch ? “ irin wanda yake hanun ka,yafada tare da nuna masa diamond watch din dake hanun sa, cikin gam suwa da bayanin sa Ashman yace “ok. Maida system in gabansa yayi ya cigaba da abunda yake yi cikin kware wa irin na wayanda suka jiku da bokonan ,,anan ya gano location din da suka ajiye junaid,a zuciyan sa yace wannan daga gani kwakawal wansa bata fada masa dadai, ka dauke mutum kaman junaid kuma ka barsa a kasar USA Hmmm. Ta agogon dake hanun junaid ya gano inda aka yake ,saboda yasa abun bin diddigi saboda irin hakan. Fita Ashman yayi ya bawa “boss lion “ waje dan y huta dan sai yanzu hankalinsa ya kwanta,yana fita “boss lion”ya shiga wanka ya fito yashiya ya zauna ya fara wani aikin kuma. Sai da suka bata 6hrs kafun sukayi niyan tafiya dan Süha wani mai kararren kwanan ne yake son ganin “boss lion”, A Jere motocin suke tafiya gwanin burgewa yanda sukayi convoy duna tafiya. Lokacin da suka isa ne ,sukaga a wani un complete building ,babu bata lokaci sojojin suka shiga suka farmakesu, sun tarar suna kokarin harbin junaid din. CIGABAN LABARI 💃 Bayan sun shiga ,kowa ya wuce dakinsa domin yayi wanka ya ci abinci a huta. “Boss lion” Yana shiga dakinsa ya Rage kayan jikinsa ya daura towel a kugunsa ya wuce toilet bai wuce 30mins ba ya fito ,dan shi fah komai na rayuwansa a lissafe yake yinsa ,every minute have his time ,babu wani abu shi African time su a rayuwansu ,komai zai ware masa nasa lokacin. Fitowa yayi daure da wani towel a kugunsa ,daya kuma yana goge curly hair sa ya wuce dressing room within 10mins yafito jikinsa sanye da three quarter white and white t-shirt shima white color na kamfanin gucci bakaramin kyau Allah yayi anan ba (dan nidai kam ban taba ganin kyakyawa irin sa ba sai dai muce masha Allah ) ga curly hair sa yasha gyara sai shining yake yi, alamun ba karamin dollars yake sha ba. Fito wansa kenan yaji ana knocking har sau uku kafun a hankali yace yes ,dan ba Lallai wanda yake knocking din ya jishi sosai ba,amma shi ashman din yaji shi dan yasan halin yayan nasa. Shiga yayi hanunsa dauke da golden color trey mai kyau dauke a hanunsa da sallama a bakinsa ,junaid na biye dashi a bayansa ,a jiye trey yayi akan center table ,shikuma junaid wuce wa yayi wajen “boss lion” ya fada jikinsa har zai zame “boss lion” yayi saurin dawo dashi jikinsa. 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 15 Bayan fadawa jikinsa junaid yace “yayana” yakai wajan 2 mins kafun yace Uhmmm a hakan ma wai dan junior sama , danne dannen sa yake yi a iphone 16 latest version hanunsa kuma yana kan junaid yana shafa lallausan gashi junaid daya sha gyare sai yalki yake yi, “yaya ni yunwa nake ji fah”,, “ yanzu kai junior bakasan inda abinci yake bane kokuma dai kawai dadi ne da yayi maka yawa”uhm uhm nidai yunwa nake ji,kuma tare da kai zamuci “to na Hana kane junior “boss lion “ ya fada. Wani munafukin murmushi ne ta kub cewa Ashman yace” Lallai yaro ai da yanzu sai dai kaci a barzaku,mukuma Muna amsan gaisuwa ,sai dai muy tacewa ohh junaid da yanzu yananan da anyi kaza da kaza. Cikin kulawa junaid ya maida kallansa kan “boss lion” ya shagwabe fuska kaman zaiyi kuka yace “yaya kanajin abunda ya Ashman yake fada mun ba ,Allah kace ya dai na banaso ya fada hade da turo karamin pink lips nashi . Kara tamke fuskansa “boss lion “ yayi Dama kullum fuskan a tamke yake ,ya jefawa Ashman wani mungun kallo yayi, ,a take ya Dena dariyan daya ke yiwa junaid ,yace Shikkenan na daina. Saving nasu Ashman ya fara yi ,bayanan ya zuba suka faraci a hankali kaman basaso. Cikin farin ciki da kaunar juna. ___________________________________________🫶 Gombe , Yau saura kwana hudu daurin aurenta,a fadan su innah tarasa yanda zata bullowa al’amarin ,sai dai ta zauna tayi kuka kodan zai rage mata abunda take ji , duniyan tayi mata zafi har rama sai data yi saboda damuwa . Yanzu ma zaune take a daki tare da zulaihat Tana bata shawara marar kan gado, da rashin illimi. Zulaihat tace ni a ganina kawai ki yarda ki auresan wata kila gidansan zaifi miki dadin zama fiye da nan kumafa idan kinaso zaki iya gyara sa tunda kinga ai yana sonki. Wani banzan kallo SULTANA tayi ma zulaihat irin na baki da hankali tace “ amma dai zulaihat kanki akwai motsi ko dan wannan ba hujja bace da zaisa na auresa ,ke yanzu koni nace na amince zan auresa ,ai sai ki hanani gudun fadawa halaka,amma da bakinki kike cewa nayar da Hmmm ta jijjiga kai tace” over my dead body I swear. Nifa bazan taba zama a auramun wannan abun da ko hankali bashi dashi “inaaaaa ai kema maganan kikeso “da in auresa gwanda na shiga duniya kowa ma ya huta dan makiyana haka suke so ,amma a koni lokaci ta tsinci kanka cikin wani hali sai kace Alhamdulillah “ dan kafi wasu ,wasu sun fika ,wani wahalan danake sha bai daukesa komai ba akan wanda shiyake ciki“amma da hankali nakam a’a sai dai ko ke. Kallonta zulaihat tayi tace lallai kam kin raina mun hankali ,harda wani cewa ko ni ,na miki kama da wacce zata auri wannan abun ,kedin dai da’aka ce ke zaki aure sa badai ni ba,ta fada tare da fita daga daki cikin jin zafin abunda SULTANA ta fada mata,kuma abunda yasa take jin zafin SULTANA saboda yanda su inaah,adda Habiba,adda deeje kullum suke hure mata kunne suna cusa mata kin SULTANA a rai har tazo ta yarda da abunda suke fada. SULTANA nakam sake baki kawai tayi tabi zulaihat da kallo har ta fita daga dakin ,ta rasa meye yasa zulaihat ta canja daga yanda ta santa,Dan da dai ba haka take ba tana sonra tana bata kulawa fiye da kowa. Kuka ta fashe dashi mai tsuma zuciya ,tana san wata rana kafun ta mutu a taga ana nuna mata so tama taji yanda mutane suke ji”share hawayenta tayi ,ya mike tsaye . Jikin dan karamin madubin daki taje ya tsaya tana kallon kyakyawan fuskanta a jikin madubin daki “fukanta yayi fayaw dashi na raman da tayi ,sai blue eyes nata masu kyau da sheki ,tayi wani haske kaman ka taba jini ya fito , kana ganinta kaga balarabiya dan a haskenta babu misk da baki. Ajiyar zuciya ta sauke ,ganin duk abunan bashine mafita a gare ta ba yasa ta dauki hijab nata ta shirya ta fita ta wuce gidansu aneesa dan tanajin daga yau ba Lallai ta sake zuwa ba ,saboda inaah ta mata warning. Wai kar tasa mutanen anguwa su zageta,ace aurenta saura kwana hudu amma tana fita aikin ,saboda tariga ta takarbe kudin aikin nata shekaran jiya ko bari batayi ta shiga dakiba ta miko hanu wai”miko mun kudin dan inada abunyi “ga shirye shiryen biki yana kara matsowa,babu musu ya bata kudin tawuce daki da sauran kudin daya rage mata. Bayan ta isah ta shiga cikin gida ,shikuma jabir zai fita da mota ,ya sha gabanta , sauke glass in motan yayi yana jifanta da wani mungun kallo,rabonta dashi tun ranan da ta buga masa bedside lamp bata sake ganin shiba ,har yanzu da bandage a kansa dan bai warke,da mommy ya tambaye sa waye yamasa wannan abu”cewa yayi bugewa yayi da asuba aka dauke wuta bai sani ba ya buge kansa. Kallanta yayi “yayi murmushi yace kina tunanin ki bugeni a banza ne ? Hmmm wannan karyane ,kin gannin nan bana yafiya saina jefah rayuwanki a cikin garari ,inda zaki bode idanunki kiga ba wanda kika sani bare ki samu mai taima kon ki bata ce masa komai ba dan damuwa da take ciki yafi wanda yake fada kuma bata wani maida hankali akan abunba. Harya juya zai tafi kuma ya dawo yace”oohh sorry na manta banyi congratulating naki ba Ashe gatane auren , abunda kike hanamun dai dan damane ma zai samesa a banza,Shikkenan dai sai munzo daurin auren”ya karasa magana yana dariyan shakiyanci ,yaja motansa yafita. Cikin tsoro SULTANA take ganin sa har yafita daga gidan”yanzu yana nufin kowa na gidannan yasan auren da za’ayi mata ,,dankuwa yanda jabir ya sani ba abunda zai hana bai fadawa kowaba a cikin gidanan ,ji tayi kaman ya koma inda ta fito dan takaici da kunya ace dan daba kuma dan shaye shaye zata aura. Daurewa kawai tayi tashiga gidan a falon kasa ta samu aneesa zaune kaman tana cikin damuwa . Shigowanta ne yasa Aneesa dagowa dan taga wanda ya shigo,tana ganin SULTANA ne tayi sauri taje ta rungume ta ,,ta fashe da kuka tace “SULTANA shin da gaske ne abunda ya jabir ya fada mana cewa aure zakiyi nan da kwana hudu kuma dan daba ,,tana magana hawaye yana sauka daga idanta dan abun ya bata mata rai sosai ace kaman SULTANA ace za’a aura mata dan shaye shaye ai wannan cutanta kawai za’ayi. Bubbuga bayanta SULTANA tayi cikin rarrashi tace ki kwantar da hankalinki Insha Allah baza ayi auren nan ba muddin ina numfashi a doran kasa abunda nake so dake shine addu’a Allah ya kawomun mafitan yanda zayi kiji. Gyada Kanta Aneesa tayi,dan sai yanzu hankalinta ya kwanta dataji abunda SULTANA ta fada mata ,dan Allah Allah take yi safiya tayi taga sultana suyi magana. Kije ki kwanta kiyi bacci kafunan na gama break fast dan nasan ba wani ishashen bacci kikayi ba “ba inda zanje ,kawai muje kitchen in na taya ki aiki “a’a dankin baride kinje kin kwantan zaifi “ Kawai ki bari tunda ni nace zan taya ki”gyada kai sultana tayi suka wuce kitchen cikin kankanin lokaci suka gama abun karyawa ,Aneesa ta wuce daki dantayi wanka. (Saimun hadu ranan Monday idan Allah ya kaimu). 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 16 AFTER SOME HOURS 2:33pm Ta gama abincin rana mommy ta fita anguwa tare da zainab da Aneesa amma dai sunyi sallama da aneesa “zainab kam tana ganinta Taita dariya harda habaici “ohh Duk wannan kyau din duk yanganan dai akan dan shaye shaye zaki kare “mudai zamuzo cin abincin biki “bakaken maganganu taita fada ma sultana kuma abun takaicin ma agaban mommy ba abunda tace sai ma dariya datake yi alamun itama abun ya mata dadi ba dan kadan ba. Tana zaune a falo tana ganin tv ,idan ka ganta zakiyi tunanin hankalita yana kan tv ne amma sam ba haka bane tayi zufi cikin tunani. A hankali khalifah ya isa wajan ta,wanda dawo wansa kenan daga office ,,sunanta ya kira”Sultana,Sultana Sultana har sau uku kafun ta firgita daga tunanin data tafi kallonsa tayi ,,da mamaki akan fuskanta dan bai taba mata magana ba agidan . Cikin nutsuwa yace zamu iya magana ,sai datayi dan Jim kafun tace eh “zama yayi akan one seater dake facing nata yayi gyaran murya yace”maganan da zamuyi tanada matukar muhimmaci kidan bani aron hankalin ki ,dago Kanta tayi ta kallesa, ta gyada masa kanta “dan shi fah kalifa kyakyawane black beauty dan yafi jabir kyau nesa ba kusa ba dan munin mahaifiyasa jabir ya daukko tareda zainab kawai dai su farare ne farin mahaifiyar su suka dauko. Yace “ shin abunda jiya naji jabir ya fada mana gaskiyane? Cikin jin ba dadi tace eh gaskiya ne ko akwai wani abune,gyara zamansa yayi yace “amma dan Allah karki yarda ki auresa dan kinfi karfin auren irin wayanan mutanen “cikin mamaki Sultana tace saboda mesa zaka ce hakan”saboda ina sonki,tun ranan Dana fara ganin ki sonki yaymun dirar mikiya please ki Fasa auren wannan abun . Ki aureni nutkuma Zan baki gata da kulawa da duk mata take bukata a gidan mijinta karkiga laifina ,kullum dake nake kwana nake tashi , kisoni ko kadanne please,ya karasa maganan muryansa a rarrabe . Cikin tausayinsa sultana tace kayi hakuri banida wani zabi daya wuce na auresa ,bawai dan bakamun ba”a’a kawai dai banajin hakan mai yuwuwane dan haka ina maka fatan alkairi,tana gama fadan hakan ta miki ,shima cikin sauri yamike yana cewa”please sultana karki mun haka dan Allah. Girgiza kanta tayi tace” kai zan bawa hakuri please ka ajiye wannan magana a gefe tana fadan haka ta koma kitchen ta barshi tsaye kaman an dasashi yakasayi kwakwaran motsi. Kashe gas din tayi ,ta sauke tukunyan ta juye ruwan zafin flask ta ajiye ta gyara zaman niqab dinta ta fita daga kitchen din,a falo taga Khalifa a tsaye a inda ta barshi tanufi hanyar fita bata cemasa kalaba tayi ta fiyanta ,shikuma da ido ya rakata dayayi jaaa sosai . Komawa tayi gidan dan bata tunanin daga yau innah zata kara batinta ta fita,abun takaicin ba abunda zata, ma ta na alkhairi sai ma sharri. Tana komawa gida ,ko minute 5 batayi ba wani yaro yashigo yace “ana kiranta a waje, ammasawa tayi da”toh, ta gyara hijab dinta ta fito waje ,a bakin kofan gidan ta samu garbati tsaye ya na busan taba ,harkan fuskanta,tuni ta hada rai ,cikin masifa tace wanna wani irin dabbanci ne yake damunka,zakana fesamun hayaki da kuma warin tabanka “duk wanda kasha a waje bai isheka har sai kazo gidan,kuma har kan fuskana saboda wulakanci. Haba beb ko gaisuwa babu zaki hauni da masifa , gani nayi ya kamata ki saba tunyanzu kafun mushiga daga ciki ,kuma dakike cewa “nayi miki wulakaci ai ba abunda kika gani ,a cikin abunda na iyah,sai nan da kwana hudu daurin aurenmu zaki zama halaliyata anan zaki gane na’iya wulakanci “ki shirya fah dan zamuci “uwar sabada a daren farkon mu “duk dama dai nasan kema yar hanune. Cikin bacin rai tace kagama ,kwai kuwa my beb ai je ta dabance kinsan ni mai sa’a ne gashi kuma zan auri balarabiya wai duniya tayi mun dadi ya fada cikin nishadi. Ka ajeye wannan a kanka “kaganin nan ta fada tana nuna kanta tace”wallahi nafi karfin ka ,irinku ne fa ya kamata ace yanzu ma kuna gidan yari,insha Allah “sai gani sai hange ,hangen ma idan kasamu kenan “saboda bakada kunya harni zakazo kanamun maganan banza “toh bari kaji karka sake zuwa gidanan da sunan kazo waje na ,dan zan maka rashin mutuci wallahi. Ko akan hanya ka ga mai kamata ka canja hanya dan nikam bazan dauki rainin hankali ba “Kaje can ka karata da shaye-Shayen ka ,kaji na fada maka . Tana karasa fada bata sauraresa ba tayi koma wa ta gida ,ta barsa sai masifa yaki yi kaman ya ara baki. ___________________________________________✍️ Abuja,Nigeria Kwance take akan gado sai juyi takeyi takasa bacci ,gashi gobe da wuri zata tashi dan zasu raka ya alameen airport dan hutunsa har ya kare,tana jin ba dadi cikin ranta zai tafi dan duk abunda yake mata tanason yayanta kuma shima yana sonta,kawai dai muddin suka hadune sai sunyi fada koda kuwa abun bai taka kara ya karya bane. Taya ma za’a ce basa san junansu bayan suna uwa daya uba daya . Cikin ikon Allah bata san lokacin da bacci ya dauke ta ba . Washe gari Ta danso ta nakara sallan asuba dan bata samu bacci da wuri ba jiya ,Allah ya sota ma yau weekend ne ,tashi tayi tashiga toilet tayi alwala tayi sallah . Shiyawa tayi cikin dogon rigan atampha nevy blue and ash dinkin irin fitted din nan ne daidai Jikinta da akwai shape kam ba kaifi tayi daurinta mai kyau ,Masha Allah tayi kyau kaman ka saceta ka gudu. Daukan ash gyale tayi ta fito dashi a hanun ta dan jirginsa 7:00am zai tashi gashi yanzu har 6:33am tayi ,,a falon kasa ta samesa da shida Ammi dan yanzu macewa yake “wai Ammi yariyar nan bazata fito bane saita batamun lokaci . Cikin sauri tace ganinan yaya ina shirya wani,batar da yaganta ba yace ki dakko mun akwatina a daki ,kisame mu a mota,ta amsa da toh ,shikuma ya wuce parking space. Gurin Ammi taje tace,”good morning Ammi “cikin kulawa ammi tace” morning daughter “ kintashi lafiya”,lafiya kalau ammi ,toh kije ki daukko masa abunda ya aike ki Nima ganinan zuwa,idan yaso saiki samemu a parking space”kinji? Eh baji ammi. Dakinsa ta wuce taga karamin a kwantin a kan gado ta daukko ta fito ta samu har ammi ta wuce,itama sai ta fita . Ta samesu a cikin motan ammi tana baya ,ta bude motan tace”yaya alameen ka budemun boot in din na saka akwatin,bude wa yayi batare da yace komai ,ta bude ta saka yashigo sai a lokacin yaga irin kayan data saka dan tayi mishi kyau amma yashi zafi yanda ammi bata mata magana akan kayan ba ta fito a haka kamar arniya. Shiga tayi yaja mota da gudu har Ammi tana cewa”sannu alameen harka gaji da ganin mu kenan kakeso ka kashemu,cikin kwantar da murya yace ammi kiyi hakuri baza’a sake ba. A haka har suka isa Nnamdi Azikiwe International Airport sauka sukayi dan har an fara kiran passengers dan sunyi latti ,daukan akwatinsa suka yi sallama da ammi “alameen dan Allah akula banda kula abokan banza ,ka tsaya kayi abunda ya kaika kaji,,Toh Insha Allah “Yauwa Allah yatsare ya bada abunda akaje nema ,,saduwan alkhairi “Ameen ya amsa. Shukrah ma tace yaya Allah ya kiyaye hanya sai yaushe zaka dawo “hararanta yayi yace”Ameen amma dai nasan dama Allah Allah kikeyi na tafi dan kina ganin kaman ta kura miki nake ,yanzu saboda Allah kiga irin kayan da kika saka tsa kani da Allah kin kyautawa kanki kenan ,yayi kasa da murya yace please koda banan karki sake sa irin wayanan kaya koda a gidane dan bakisan wa zai shigo “kinji? Eh yaya alameen insha Allah bazan sake ba “good sai na dawo kuma badda rashin ji please bye “Insha Allah tace tare da daga masa hannu ya wuce. Ammi kam tana cikin mota batasan me suke fada ba ,sai da ya tafi kafun ta fito tawuce driver site ta zauna ,shukrah tana zauna a kujeran mai zaman banza ammi ta ja motan suka wuce gida. 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 17 Yau saura kwana daya daurin aurenta damuwa da rashin mafita ne ga kuma rashin cin abinci ne ya sata agaba har tayi wani uban rama tayi wani fayyaw,sai haske data kara tass da ita kaman jini ya fito,ga kashin wiyan daya fito mata saboda rama. Tayi kukan ,tayi kukan har ta godewa Allah,gashi ba mai kulata a gidan ,dan ko zulaihat da take kulata yanzu ta daina ,abun ba karamin damunta yake yi ba “tariga da ta yake shara datake ganin shi zai fisheta . Habiba ce ta shigo daki ba sallama ba komai ,cikin rangwada da iyeyi tace,sai ki tashi kije babba yana kiranki munafuka aurene dai sai anyi sai dai bakin ciki ya kashe ki ,dan mu kokin mutu ba’abun daya damenu,tan tarasa fada tafice daga dakin tare da jan dogon tsaki tabar dakin. Mikewa tayi ta dauki hijab nata dake gefenta tasaka ta fito daga saki,gidan shaw ba kowa ,kumawai a haka gobe ne daurin auren . A kofan dakinsa ta tsaya tayi sallama kafun ya bata izinin shiga ciki ,shiga rayi ta samesa zaune akan taburman dake shimfide a tsakiyan dakin,ta durkusa har kasa ta gaishe shi. Bayabo ba fallasa ya amsa,tsayawa yayi kawai yana ganin ta yana saka wani abu a ransa,danshi wallahi bai tsaneta ba kawai dai indai zai ganta ne,zaiji kwata kwata baya dinta a kusa dashi. Gyara murya yayi yace”ga wannan kayan,gobe kishirya dan na daurin aure ne,idan yaso saiki saka wannan din,dan shikadai na samu na iya miki ,dan babu kudi a wajena . Cikin jin dadin koba komai dai yau ya kulata irin na shekarun baya ,daga bayane ya daina kulata,kuma tariga da tasan wannan ba yin kansa bane aikin innah ne,shiyasa bata wani jin zafin abunda yake mata,cikin sanyi murya tace”abba Nagode hakanma kayi kokari,Allah ya saka da alheri ya biya maka da gidan aljanna. Cikin jin ba dadi idan ya tuna abunda yayta mata yace”Ameen nagode da irin biyayyan da kike nuna mun sabanin sauran yan uwanki”Allah ya miki Albarka a duk inda zaki tsinci kanki,ki kara mutuncin ki dan nasa kına iya bakin kokariki amma dai ki kara kinji. Muryanta yana rawa irin wanda yake shirin fashe wa da kuka tace”Ameen abba Insha Allah bazan baka kunya ba,bata karsa ba hawayen datake rikewa ya zuba mata a kan fuskanta,tayi saurin sharewa dan kar abba ya gani,amma abunda bata saniba yariga da yagani yace”kiyi hakuri nasan na kasa sauke nauyi daya rataya a kaina wajan zaba miki abokin rayuwa na gari,ki yafemun nima bada son raina hakan zai faru ba ,bayanda na iya ne. Yaken dole sultana tayi tace “bakomai abba ai kai mahaifine a gareni,ni mai biyayya ce a gareka,dan haka karkasa komai a ranka,jiyayi an yaye masa rabin abunda yake masa nauyi a zuciya”Shikkenan zaki iya tafiya . Toh tace tare damike wa tafita daga dakin,ta koma dakinsu daya har lokacin sallan azahar yayi, alwala tayi ta koma dakinsu tayi sallah ,sai data dade a sujjada tana kaiwa Allah kukanta “ya Allah na rokeka kanema mun mafita,ya Allah kaga zuciyar wannan baiwar taka batasan wannan auren “ta dade tana addu’a harda hawayenta ta daga hannunta sama ta rikoki Allah . _______________________________________________🙏 AFTER SOME HOURS 🤧 Bayan isha, Kwance take akan gado bacci ya dauketa ba tareda ta shirya ba,soboda kukan da tasha ga rashin baccin dare ishashe da bata samu tanayi saboda damuwa, ta dukun kune a cikin hijabi tana rawan sanyi ,alaman zazzabi ne ya rufe ta. Yarone yashigo cikin gidan ,lokacin ina suna zaune akan taburma dan kullum da daddare a waje suke zama hira ,wani lokacin ,idan da zafi a waje suke kwana amma badda sultana komin sanyi haka komin zafi a cikin daki take kwana. Yaron yace”ana sallama wai da sultana a waje, tane baki innah tayi tace “inji waye ,”ban sani bazai amma bari inje na tambaya, bayan 1 minutes ya dawo yace “cewa yayi garbati ne”toh kace masa tana zuwa yanzu” Uhmmm yace ya fita daga gidan. Innah ta kali zulaihat tace”Kira wannan munafuka kice mata tazo tawuce mijinta yana kiranta a waje,kuma saura ta bata masa lokaci jikinta ya gaya mata”cikin zumburo baki zulaihat tace”nidai innah ba inda zanje dan nii bana mata magana,dan nafi karfin ta class namu ma ba daya bane,takarasa maganan tare da jan tsaki. Ba abunda ina tace ,kafun ta kalli deeje dake latsa waya tace toh ke deeje kije ki mata magana “deeje ta bata rai tace”innah har zulaihat zata ce miki ta fi karfin ta bare kumani ai basa’ar ta bace” hmmm bare kumani Habiba ta karbe zancen alamun tana ba tashi zatayi ba,cikin washe baki innah tace Yauwa yan albarka ,dama abunda na dade nake son fada muku cewa ba sa’arku bace dan kunfita komai”ba wanda ya kuta a cikinsu kowa harkan gabansa yakeyi,ganin hakan yasa tamike tace”bari naje na fito da ita ,ta fada tare da wuce dakinsu SULTANA. Tana zuwa ta ganta kwace a kan gado cikin masifa ta İsa kan SULTANA dake rawan sanyi tace”munafuka zaki tashe kije ana kiranki na ko kokuma ranki inyayi dubu to sai ya baci, baiwar duk bataji abunda ina take fada ba,bacci nata yayi nauyi. Ganin bata kulata ba yasa innah jan kwafa ta fita tabar dakin ,bayan 2 minute sai gata da roba a hannu na ruwan da suka shanya dan yayi sanyi,tana zuwa batayi wata wata ba ta juye mata ruwan gaba daya a jikinta ,gashi ruwan yanada sanyi. A firgice SULTANA ta tashi tana fadan”inalillahi wa’inna ilaihir-raji’un,,Allahumma ajirni fi musibati, bakinta kawai ta iya fada,ta mike daga kwancen da take ,tabude idonta da sukayi jaah kuma sukayi mata nauyi akan innah dake ta huci kaman zaki. Zaki tashi ne ,kokuwa tsayawa zakiyi kina kallo na da mayun idanunki ,a hankali ta mike da harwani jiri jiri take ji,”ki wuce kije kin bar bawan Allah a’a waje ,tana kara fada ta fita daga daki. Cikin sanyin jiki da kuma zazzabin dake damunta sosai ta cire kayan da ya jike ta saka wani materials na dogon riga,ta tacan ja hijab ta fita daga dakin dan har yanzu jikinta rawa yake yi ,wuce su tayi ba tare da ta kalli inda suke ba. Tana fita ,sai kuma bata ga kowa ba layin ba mutum ko daya a waje ,juyawa tayi zata koma taji an danneta an shaqa mata abu a hanci,daganan bata sake sanin inda kanta yake ba. Mutumin da ya shaqa mata abun ne ya dauke ta ya kaita har cikin mota,ya saka ta a ciki yaja motarsa ,gashi bakaken kayane a jikinsa . (Ohhh jama’a ina za’akai mana sultana baiwar Allah,daga wannan jarabawan sai wancan) 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Follow this link to join my WhatsApp group: Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 18 Tafiya sukayi mai nisa,tafiyan kwana daya ,kafun ta farka daga suman da tayi saboda chamical in da suka shaka mata, Zazzafan zazzabi ne daya rufeta. Tashi tayi ta zauna da kyar,abunda ya faru jiya daddare ne ya dawo mata yasa cikin sauri ta fara dube dube,ba kowa daga ita sai mai driving na motan da batasan kowaye ba ,ga yunwa takeji kaman da ta mutu. A hankali ta isa jikin murfin motan,ta murda kuma bai bude ba,hakan da tayi ne ya ankarar da wanda yake driving akan ta tashi kenan,bai kula taba saida suka samu wajan siyar da abu ya tsaya ya siya ya koma cikin motan. Kuka ta fashe dashi mai tsuma zuciya dan,ba’iya magana zatayi ba,batada karfin yin magana,ji takeyi kaman ta kurman ce ,zata iya bude baki amma bazata iya magana ba sai dai tabika da ido. Mika mata ledan akayi batare da taga fuskansa ba,da sauri ta karba dan Yunwa take ji,bude ledan ,fried rice with chicken ne a ciki ,Bismillah tayi a zuciyanta ta fara ci ,tacı fiye da rabi kafun taji zuciyanta yana tashi,ta bubaga masa kujera ,juyowa yayi yana ganinta ya gane me take nufi yasa ya bude mata murfin motan ta fito”tana fitowa kuwa ta fara amai kaman an aikota ,ruwa ya Mika mata ta wanke bakinta,suka koma cikin motan ,suka cigaba da tafiya. Tafiyan hour 3 suka kara kafun suka shigo cikin kasar niger 🇳🇪 direct airport ya wuce da ita,a lokacin karfe 7 na safe a kasar niger,Mika mata passportyayi, batare da musu ba ta karba ,ji takeyi kaman asiri yayi mata ,bata iya yi masa musu. 7:30am jirgin zai tashi zuwa wani kasar,time yana cika,aka fara kiran passengers suna shiga ,waje daya suka zauna tare da wanda ya dakkota a mota,a gefen site nasa ta zauna. Tafiya 13hrs 42 minutes sukayi kafun suka isah USA 🇺🇸 ,bayan sunyi landing passenger suka sauka ,taxi ya tara musu,suka shiga ,SULTANA abun har yayi mata yawa ga zazzabi ,damuwa,rashin ma fita,gashi gari sanyi kaman ka daskare. A wani gida suka tsaya mai girma ginin turawa,suka shiga ,yan matane da samari kala kala,kowa da kalan shigan dake jikinsa ,mazan wasu da three quater,wasu kuma dogon wando jeans,matan kuma mini skirt da riga iya cibiya ko boom shot,bra and pant,kowadai da irin shigan da yayi,alama dai gidan karuwai ne. Shiga cikin wani falo mai kyau sukayi,a Kwai maza da yawa aciki ,sai mutum daya dake zaune akan kujera ya juya baya,suku ma sauran a tsaye suke wasu kuma a zaune akan kujeran falon. Tunda suka shiga jikinta ya fara rawa kaman mazari,ganin wanda batayi tsammani ba”sai yanzu ta samu ta iya furta “innalillahi wa’inna ilaihir raji’un”kafanta ya gagara daukanta ji takeyi dama ta mutu kowa ma ya huta. Mikewa wanda da ta gani yayi ,ya matso har inda take ba kowa bane face JABIR sanye da three quarter da bai kai gwaiwansa ba, wani askin yan iska yayi tare da die hair sa zuwa red,yellow,green ,ga wasu sarka a wuyansa kaman kafuri,kana ganinsa kaga tantirin dan iska. Tsugunnawa yayi a gabanta tare da cewa “hey baby,yau ina jijji dakan naki yake ,dama na fada miki dan halaq kafasa,kuma abunda kike boyewan ma muma sai mun dan dana munji, tare da abokan harka ta”koba haka ba guys” Yes jab ,mikewa yayi wakoma inda yake zaune Dazu ,ya dauki telephone in dake falo yakira waya banji mai yace ba “ko one minute ba’ayi ba saiga wata jigegiyar mata baturiya tashi go cikin falo. Direct inda take matar ta nufa tace “tashi muje”ba musu sultana ta tashi tana sharar kwalla dake zobo mata kaman famfo,bata taba tsammanin tsanan da jabir ya mata yakai haka ba ,kawai saboda san zuciya irin nasa yasa ya dakko ta daga gidan ubanta ya kawota gidan karuwai. Wallahi kozasu kashe bazata taba basu abunda suke soba,wani part matar tanufa da ita ,duk yan matane a part din yawanci daga su sai pant,da bra ne a jikin su. Tunda suka shigo cikin falon yan mata suke mata kallan raini,daga karshe ma da abun ya isheta ta sunkuyar da kanta ,bata sake kallon kowa ba har suka shiga wani daki yan mata uku ne a dakin,gado hudu ne a dakin nuna mata gadon da ba kowa tayi tace”wannan shine dakinku ga gadonki”cikin sanyi murya SULTANA tace toh ,nemi waje ta zauna dan jiri takeji anytime zata iya faduwa. Abinci matar ta fita ta kowo mata mai rai da lafiya ,kara tayi taci amma duk da haka saida tayi amai,ba wanda ya kulata a cikin yan matan dake dakin kowa harkan gabansu sukeyi. Wanke bakinta tayi kafun ta fito daga toilet in ya kwanta akan gadon da wancan matar ta nuna mata sai rawanan sanyi take,zazzabi ne ya take rufeta mai bala’in zafi “Tana blanket in data gani akan gadon taru fu. ________________________________________________✍️ Yau kwannan ta biyu za zuwa, jikinta yayi tsanani,gashi babu wanda ya taba kulata a cikinsu ,sun hade kansu basa mata magana,abun ta kaicin ma”wani lokacin sai dai taji gurnanin su da ihunsu,idan suna neman junan su wato lesbian ,yanzu kamma hawayenta sun kafe idanunta sun kumbura suntum . A na kawo mata abinci,ko taci sai tayi amansa,ta rame sosai ,sai haske kawai da take yi.tunda aka kawo ta bata sake haduwa da jabir ba . Damuwanta shine yanda zata samu hanyan guduwa daga gidan,dan ta tabbatar idan aka kamasu,ba wanda zaice badda ita a cikin karuwannan. Akwai wata black beauty a dakin nasu , ba ruwanta da shiga cikin yan mata biyun nan,dama tun kafun SULTANA tazo take rayuwa ita kadai abunta ,batada kawa ko a boki. A hankali hakuwa ya fara shiga tsakanin ta da SULTANA,saboda ganin yanda take kwana ta tashi da zazzabi ne yasa ta tausaya mata ta tambayeta meya same “cikin karfin hali sultana tace wallahi zazzabi ne yake damuna,ji nake kaman zan mutu. Cikin tausayawa back beauty tace Allah sarki ,Allah ya baki lafiya ,meye sunan ki”SULTANA “suna mai dadi,kefah sultana ta tambaya ,ni sunana ilham can we become friends,cikin jin sanyi sultana tace”why not “ dan koba komai za tayi amfanin da wannan daman wajan samun mafita a gidan anan. Tun daga wannan lokacin sultana da ilham suka zama ka waye,ko yaushe suna tare ammafa duk da haka sultana tana fama da zazzabi ,da haryau bai warke ba. Zaune suke a fillin babban gidan suna magana inda sunan ganin duk wani mai shiga da fita a gidan,kuma security basa hana kowa fita wajan karuwancin sa,jikinsu sanye da dogon ruga ba’a ganin jikinsu,sultana kam da hijabin ta da tazo dashi kullum yana jikinta ,bata iya rabuwa dashi. Sultana tace”amma ilham bakya tunanin guduwa daga wannan gidanne ,dan naga kowa yana iya fita,ban taba ganin kin fita daga gidan ba ,tace hmmm”sultana kenan ai sunsan wayanda suke bari su fita dan ba karamin tsaro suka saka ba. Yanzu kina nufin a gidanan zamui ta zama kenan “eh toh zan iya nema miki hanyan da zaki iya guduwa amma nikam ko na gudu bani da inda zanje. Kina nufin bakida wanda kika sani a cikin familyn iyayen ki,”ai sune ma suka kawoni wannan wajan wai bazasu iya rike maraya ba,cikin tausayinta sultana tace kiyi hakuri ilham ,komai mai wuce wani”Insha Allah ilham ta fada” Mikewa suka yi suka wuce cikin dakinsu. 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 19 7:22pm Junaid ne zaune akan kujeran dake indoor,yafito hutawa,sanye yake da jallabiya milk color a jikinsa yayi masa kyau,gabanshi a Kwai abun tabawa a gabansa. Wayansa ne yake ringing,yasa hani yadauka,sunan besty ne a jikin wajan,daga wa yayi yace suka fara magana bansandai mai besty ke fadamasa ba kawai gani nayi ya miki jikinsa yana rawa ya fito,dakin ashman ya wuce dan yasan har yanzu “boss lion” bai dawo ba. A dakinsa yasa mu ashman yana kwance akan gado da waya a hanunsa,sallama yayi yashiga,ya zauna a gefen gadon yace”yaya ash please inaso naje wajan besty ,yanzu aka kirani a waya akace yayi hatsari. “Junaid amma dai kasan wannan ba mai yuwuwa bane ko,ina zaune lafiya bazaka dakko mun masifa ba ,kawai ka koma daki ka zauna . “Please yaya ash yanzu zan dawo kafun yaya ya dawo bazan wuce 30mins ba please kaji yaya na”Shikkenan junaid kaje ka amma karka kuskura ka dade,dan yaya boss yana tambayana cewa zanyi nima bansan lokacin da kafita ba kokuma nace na hanaka kakiji sai da ka fita,dan haka saika kuka da kanka. “Insha Allah ma hakan bazai faru ba,bye saina dawo”ok kadawo kafun ya dawo fah,Toh ya fada ,yana fita daga dakin. Fitowa yayi sojojin da suke gadainsa suka dauko wata mercedeze benze 350 ,junaid ya shiga sukuma suka shiga bakaken jeb nasu suka tafi. Junaid da kansa yake driving na motan sukuma suna binsa a baya,gashi sai gudu ya keyi dan ya isah asibitin da wuri ,su samu su koma kafun “boss lion “ ya dawo ya samu ba sanan. _________________________________________😉 8:00pm Kance SULTANA take akan gadon ta ,jikinta yayi tsanani tunda ta tashi daga baccin safe,take amai gashi ta kasa cin komai,ba wanda yake kulata,kuma sunsan batada lafiya. Ilham ne zaune a gefen ta ,tana ta mata sannu cikin tausayawa,ganin ba wanda yake kula sultana sun barta ko ta mutu kotayi rai wannan ba damuwansu bane. A hankali ta mikar da sultana tace”sultana ki daure ki tashi ki gudu daga gidan nan ,dan wallahi kika cigaba da zama ba kulaki zasuyi ba,barinki zasuyi ki mutu ba ruwansu,dan dan bake kadai suka taba mawa wannan abun ba. Mikewa tayi da kyar suka fito daga dakin ba wanda ya gansu ,suka bi wani lungu ,sun danyi tafiya mai tsayi kafun suka isa wajan get suka tsaya,ilham tace”kiyi hakuri sultana amma ya kamata kibar wajannan dan kina bukata kilawan gaggawa ,dan haka ki tsaya anan zanje na dauke hankalinsu idan yaso saiki bi ta bayansu ki wuce kafun su ankara dake” yanzu kina nufin badake zamu gudu ba ,kuma idan na gudu suka gane cewa kice wacce ta taimakamun wajan guduwa,zasu iya cutar dake. “Dariyan yake ilham tayi tace “karki damu ba wanda ya isa yamun abunda Allah bai mun ba,dan haka ki kwantar da hankalinki ,kuma kiyi yanda na ce miki,cikin muryan mara lafiya da baya fitowa sosai tace jikinta duk yayi sanyi . Wajan get din ilham taje ta tsaya,securities uku ne a wajan ,yi tayi kam zata fita ,ai kuwa da sauri mutum biyu daga cikinsu suka nefe ta ,daya daga cikinsu yana cewa “hey hey where are you going,shiru tayi cikin tsawa ya ce bazaki bude baki kiyi magana ko saina fasa miki kai a wajan nan. Bude baki tayi tana ginisa ido ciki ido tace”fita zanyi ko akwai wanda ya’isa yanani fita ne ,”ki koma dan ba’a bamu izinin barinki ki fita ba ,cikin tsawa tace “har kaisa kace zaka hanani fita ,nagadai biyanka akeyi ,da har zaka tsaya kamun magana da gadara sai kace ubana. Dayan dayake zaune tundazu yana ganinsu ,yaga yanda yarinyar take musu a sauran tsawa kaman sa’an ninta,mikewa yayi ya’isa wajan yace”ke ilham wato wiyanki yakai yanka kin girma dole ki fara rashin kunya ,amma bari kiji ki shiga hankalinki dana dan zan kasheki kuma na kashe banza. Wannan fadan da sukeyi ne yabawa sultana daman tafiya a hankali yanda ba wanda zai jita ta wuce ba wanda ya ganta. Dan hankalinsu yana kan ilham “da gudu ta fita daga get din batare da sun sani ba. Cikin sauri ogan nasu ya juya yaga wayene ya fita da gudu dan sunji karan gudunta ,ai kuwa da sauri suka bita su biyu . İlham tana ganin lokacin da sultana tabi ta bayansu har suka sakarwa juna murmushi mai hade da hawaye dan ba karamin shakuwa sukayi ba a cikin kwana hudu da sultana tayi a gidan ba . Gudu sultana takeyi da iya karfin da Allah ya bata take gudu ,duk da kuwa a kwai zazzafan zazzabi dayake damunta ,dan kunsan gudun cetan rai takeyi,juyawa baya tayi taga sun biyo ta daga Riganta ta daga,ta kara gudun nata har ta fito babban kwalta ,amma basu daina binta ba. Saura kadan su isota gashi harta galabaita,dishi dishi take gani amma hakan bai sa ta daina gudun ba. Ji tayi mota yayi sama da ita batare da tasan ya kan ta faru,faduwa tayi kasa kanta yana zubar da jini kaman da bakin fanfoo ,tana kwance a kasa ,bazan iya gane suma tayi ne kokuma dai rai ne yayi halinsa ne dai bansaniba 🥺🥹😭🤧 Securities din da suka biyo tane suka ja dabaya da gudu suka koma ganin abunda ya faru sunsan koma wacece aka bige tariga da ta mutu,dan su fah basusan ma wasuka biyo ba ,kawai dai sunga ta fita da gudune alamun gudu takeso yi shiyasa suka biyota ,Ashe ita kamma lokacin ta yayi 🤧 (Allah sarki sultana,Allah ya ji kanki da rahma yasa mutuwa hutune a gareki , munyi babban rashi yan group🥹😭🤧) 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 Allah ya jikanka aymann. pages 📃 20 Cikin tashin hankali junaid ya taka burki,jikinsa har rawa yakeyi saboda tashin hankali,bude murfin motan yayi da sauri ya fito ,yayi kan sultana da hijab din jikinta ya fadi ,gashin kanta duya bazu ya rufe mata fuska ,ga jinin daya bata mata fuska kuma,bazaka taba iya gane sultana bace. Sauran sojojin ma saukowa sukayi daga motansu hankalinsu a tashe ,ganin Kanin “boss lion “ ya bugi a bu,sufa tsoronsu kar wani abu ya samu junaid,basu damu da ganin ya buge mutum ba. A tsugune junaid yake a gefen sultana ,hanun sa sai rawa yake yi wajan taba sultana ,tsoronsa kar ace sultana ta mutu. Hanunsa ya saka ya dauke ta ,jikinta a sake tayi nauyi amma dake suma junaid in yanada karfi dan kullum sai yayi training,umarnin boss lion ne wannan. Wani sojane daga cikinsu ya mikawa junaid hanu akan ya bashi ita ,girgiza mishi Kai junaid yayi dan bashi da bakin magana. Dan tuni hawaye ya wanke masa fuska,a bayan motansa ya sakata ya kwantar da ita ,ya shiga wajan mai zaman banza,dan bazai iya driving ba,wani sojane yashiga cikin motan ,sukayi reverse suka koma gida . Bayan sun İsa gida,da kansa ya dauke ta ya shigo da ita cikin main falon gidan ya kwantar da ita akan kujera . A falon ya tarar da uncle tareeq,uncle Ibrahim suna tsaye suna jiran dawowansa dan har lokacin “boss lion “ bai dawo ba,sai kuma Ashman da yanzu shigowansa falon bayan junaid ya ajiye sultana. Sojoji ne suka kirasu a waya suka fada musu abunda ya faru,shine dalilin dayasa suka fito suna jiran isowansu. Ashman ne ya je ya samu junaid dake tsaye yana yace”yanzu junaid abunda kayi ka kyauta kenan ,gashinan wata kila ka kashe yar mutane a banza ,tsaki ya ja cikin takaici,”Allah yaya Ashman itace ta shiga ga bana da gudu, kafun ba danna bugurki ma na bigeta,nagadai alamun biyota akayi ne shiyasa ta hau kan hanyan bata sani ba. “Amma dai kasan wannan abun bazata zauna mana a gida bai dai ko,uncle Ibrahim ya fada Yanya huci,”haba ya İbrahim wannan wani irin magana ne inadai kana ganin yanda aka kawota,kaga duk jikin kujeran can jinine kaman an ganka dabba ,uncle tareeq ta fada cikin rarrashi . Ashman kam yana tsaye yana jin abunda suke ta fada”shima a ganinsa bai kamata ka kawo musu mace gida ba dan mata a sun muna furce su,kuma suka rabasu da kowa nasu ,tundaga wannan lokacin suka tsani ganin mata a rayuwansu,ko a gidanan babu wata mace da ta taba shigowa cikin gidan nan sai yar president na kasar ne ta taba shigo ,shima bata fita lafiya ba dan sai da “boss lion “ya harbe ta a kafa dan a rayuwansa ya tsani harka da mata,ita a dole “boss lion” takeso. Yana tunanin gwanda shi akan “boss lion” dan yasan wannan maganan ma bamai yuwuwa bane,dan bazai yarda wata mace ta zauna masa a gida ba,dan haka shima bai goyi bayan zamanta a gidan nan ba . Cikin tada jijiyoyi wiya uncle Ibrahim yace,kanada hankali kuwa tareeq mace fah kuma a gidan nan ai wannan ba mai yuwuwa bane ,bari “my son” ya dawo sai na sashi dole ya fitar da yarinyar nan ,dan nasan shima bazai bari ta zauna ba, idan kuma yayi kokarin bari ta a gidan nan zai ga abunda zan masa ,dan koshi bai isah ya hanani fitar da ita daga gidan nan ba,ya karasa magana cikin ga dara,yanda kasan yasa naira biyar dinshi acikin gidan. Ashman kam gizgiza kashi yayi kawai ya tsaya yana ganinsa, sai kace bashine yake tsoron magana ma ya hadashi da boss lion ba,yayi murmushi a zuciyansa yace zanga yanda cika bakinan zai kare. Cikin tafiyan kasaita ya shigo cikin falo jikinsa sanye da farin wando da white long sleeve ya daura farin jacket akan kayan ,Tabarakallah masha Allah,Allah yayi halita a wajannan,fuskansa sanye da face masks ,ga black curly hair da yasha gyara sai sheki yakeyi kamshi yana tashi. Shigowansa ne ya ankarar da yan falon,koya yashiga taitayinsa bakajin karan motsin kowa ,falon ya dauki shiru ,zama yayi akan wani one seeter yayi crossing na legs nashi,yasa hanu ya cire face marks na fuskansa ,kyakyawan fuskan mai cike da kwarjini ya bayyana ,fuskanan a tamke ya ke ,kaman baysan wani abu shi murmushi ba bare kuma dariya ,fuskan a tamke kaman zaiyi aman wuta,dago da idonsa yayi yaga junaid a tsaye a gefen kujeran da aka ajeye sultana,yayi kifi kifi da ido irin na marasa gaskiya ,kafun ya maida idonsa kan Ashman da shima shidin yake kallo ,dauke idonsa yayi ya maida kan uncle tareeq ,kafun ya maida kan uncle Ibrahim. Ganinsa yayi kafun ya bude reddish lips nasa a hankankali kaman bayaso yace “continue what you’re saying “ya fada yana daga masa gira daya ,wannan sigh ne na zaiyi rashin mutunci,yawu mai daci uncle Ibrahim ya hadiye,ya kasa magana jikinsa har rawa yake yi saboda tsoro,nandanan yayi na daman abunda ya fada, dan kuwa tabbas yasa yaji duk abunda ya fada,dama wai shi burgansa ya musu Jan ido ,su fitar da sultana kafun ma boss lion yazo,sai koma burgansa bai yi amfani ba. Tsare sa da ido “boss lion”yayi gashi dama indai ya kalle ka da wayanan grey eyes nashi masu ladab tarwa. Since you can’t talk ,I will talk” kace zaka fitar da ita daga gidan kuma ban isah na hanaka ba,Toh Bismillah,dauketa ka fitar Tsayawa kawai uncle ibrahim yayi yana kallonsa dan bamashi da bakin magana,ya tsaya kawai yana kallon “boss lion”bakinsa yana motsi alamun magana yake yayi amma ya kasa. Please am sorry, Nifa wasa nake musu ,so nake naga sunada hankali ne kokuma dai har yanzu da sauran yarın ta a jikinsu”amma ni ni ni ya fada yana nuna kansa da yatsa ,waye ubana a garinan Dana isa nace “kafitar da ita daga gidan “ah’ah babu ba kina acikin wannan maganan. Cikin tsawa yace “nace ka dauke ta kafitar da ita ,before the count of three 3”one ……….two “jikin uncle Ibrahim rawa yake yi sosai ,kana ganin idanunsa kaga tashin hankali tun kafun yace three ya durkusa akan gwai wansa ya fashe da kuka …… 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 21 Cikin tsawa yace “nace ka dauke ta kafitar da ita ,before the count of three 3”one ……….two “jikin uncle Ibrahim rawa yake yi sosai ,kana ganin idanunsa kaga tashin hankali tun kafun yace three ya durkusa akan gwai wansa ya fashe da kuka …… “Wallahi Allah dagaske nake,wasa nake musu,kayi hakuri wallahi bazan sake kwatanta irin abunda nayi yau,”kuma ai a ganina da na kowa ne,kuma mu ne da laifi tunda junaid ne ya bugeta,Allah ya huci zuciyar lion . Junaid kam tunda yaga yanda uncle ibrahim ya durkusa akan gwaiwansa,bai san lokacinda dariya ya kwace masa ba ,ganin yanda ya zake da cewa”ko “boss lion”ne yace ta zauna bai isa ba,”huuh uncle Ibrahim a kwai dan drama”ya fada a zuciyansa”. Ashman ma abunda uncle Ibrahim yayi ya sashi yin murmushi,dan dama yasan za’a rina,indai yaya boss ne”dan ya tsana kace zaka nuna mishi isa ko kace zaka bashi umarni or kace kai sam baza’ayi wannan abun ba,annan zaku samu matsala .”dan muddin kace haka to,wallahi ko bakason wannan abun sai anyi,kuma koda shima bayaso zaiyi,dan yanuna maka kai ba kowan kowa bane.”hakan ne yasa yake ganin “tabbas boss lion “ zai bar sultana ta zauna a gidan ,badan komai ba sai yanda uncle ibrahim ya daga jijiyan wiya kan cewa ,”ba wanda ya isa yasa yariyar nan ta zauna a gidan,hakan nan ba karamin bata wa “boss lion” rai zaiyi ba. “Cikin sanyi murya yace” kasa ka kanka koda da hauka ne bada wasa ba kace zaka sake yun wannan abun ,zaka kwanane a dakin lucky “wato damusan “boss lion” bayan nan zaka hadu da punishment ina baruwa ko mutuwa zakayi sai dai kayi kaji ko” “Hakanma yayi wallahi ai ko a mafarki ma bazan sake barin haka ya faru ba. “Good, you can find your way out,ya fada cikin bada umarni”ai kuwa jikinsa ya na rawa ya wuce wajan lifter ya wuce dakin sa. Maida hankalinsa yayi kan junaid,da ya takure dikinsa waje daya saboda tsoron abunda zai biyo baya,sai kuma ya maida kallansa kan Ashman ,ya masa alama ta ido ,Dan yan miskilancin suna kusa bazai bude baki yayi magana ba. Ashman ya gane me yake nufi ne yasa “yaje wajan junaid ya daukesa a kafadansa,wanda jikinsa har bari yake yi,nan danan ya zazzabi ya kamasa saboda tashin hankali dan abune ya masa yawa,”accident na abokinsa,gana sultana ,Gana “boss lion”.”kallo daya yaya boss ya mishi ya gane shima junaid din ba lafiya yake ba ,shiyasa yasa Ashman dauke sa dan yayi mishi treatment. Bayan fitan Ashman ya saura daga shi sai sultana suka saura a falon ,dan uncle tareeq kam tunda aka cewa uncle Ibrahim ya tafi shima ya kama gabansa,dan bayason,ganin abunda zai bata wa boss lion rai. Mike wa yayi ya wuce wajan lifter yashiga,dakinsa ya shiga sai tashin kamshi yake yi mai sanyin dadi, wanka ya shiga yayi ,yashirya ciki pajamas white color mai laushi sai kamshi yake yi kaman wanda yayi barin turaren a jikinsa. Fita yayi ya wuce kitchen dan hadawa kansa coffee ☕️ dan Ashman bayanan dashi zai kawo masa,koma yayi cikin dakinsa ya dauki system nasa yana aiki,yana shan coffee sa a hankali,dan baya iya bacci idan baisha coffee ba. Sai wajen biyun dare kafun ya gama abunda zaiyi yarufe system din ya ajiye,fitowa yayi daga dakin ya koma falon kasa ,bakowa a side din ,sojojin sun koma waje dan kwana sukeyi suna aiki amma kowa smda time nashi idan wannan yayi yau Toh gobe wani ne zai yi. Direct kujeran da junaid ya ajiyeta ya nufa ,tana nan inda take ,bata motsi ,gashin nan ya baje baka ganin fuskanta ,ga jini harkan carpet ya sauka. Ya tsuna fuska yayi cikin kenkemi yasa hanu ya dauke ta ,kaman bai dauki komai ba haka yake ji. Wani daki yashiga da ita ,na hawa na hudu ,dake side nashi ,kuna wutan dakin yayi”wow gaskiya daki ya hadu iya haduwa ,pink color ne furnitures din dake cikin dakin,mai shegen kyau da tsada,yana tashin kamshi a gyare yake fess fess ,kaman wanda akayi mussaman dan ita. Kwantar da ita yayi a hankali,first eid box ya dauko ya zauna a gefen gado,tare da tattare gashin ya daya baje yayi ,fuskanta duk ya baci da jini saboda jinin daya zuba daga kanta ,batare da damuwa da jinin daya bata mata fuska ba ya fara yi mata dressing . Cikin kankanin lokaci ya gama ,batare da ya kalla gaba daya fuskanta ba,shifa inaga baya tunanin ko a hanya suka hadu bazai ganeta ba,dan jinin dake fuskanta ma kadai ,zaisa mutum ya kasa gane ta. Yana gamawa ko seconds bai kara ba ya fita daga dakin rashi duk a dagule,dan bakin ciki,wai yau shine da zuwa yayi wa wata mace treatment,kuma ya dauketa da hanunsa kai ina wallahi da sake,bayaso ya sake hadu wa da ita har ta warke ta barmasa gidan koda ko by mistake ne,zata sha mamaki,ya ja kwafa ya kashe wutan daki tare da rufe kofan. Dakinsa ya koma ya kwanta dan lokacin har 2:45am tayi addu’a yayi ya Shafa a jikinsa ya kwanta fuskanan kaman an aiko masa da sakon mutuwa,dan lokaci daya yaji wani irin tsanan ta yana mamaye masa zuciya . Dan junaid kawai yayi wannan abun,kumashi Allah ya sani ya kasan ce ba azzumi bane ,wanda za’a ce yana ganin yanda yariyar take zub da jini zai gane ba karamin ciwo taji ba,a kanta. Bai wuce 10mins ba bacci ya daukesa mai dadin gaske🥱😴 ___________________________________________😵‍💫 WASHE GARI Kiran sallan farko ya tashi ,ya shiga yayi wanka ya shirya cikin jallabiya ash color yayi mishi kyau ,dadai jikinsa dan kana ganin Moses nashi ya cikin jallabiya Dan yaya boss baidai diri ba gashi kuma ingarman na miji ,bai macen da ta’isa tasa kasa a ido tace baiyi mata ba,dan yaya boss san kowa kin wanda ya rasa, first class. Massalaci suka wuce shida ,Ashman,junaid,uncle tareeq,uncle Ibrahim ,ba wanda ya cewa kowa komai dan duk tsoron magana sukeyi dan kowa da bashi kalan laifin amma banda uncle tareeq. Suna dawowa daga masallaci dakinsa ya wuce direct dan ya kwanta,ba karamin bacci yake ji ba dan bai samu ,bacci ishashe ba,kansa har ya hara masa ciwo,jallabiya jikinsa ya cire tare da lankayawa akan hanger,yabi lafiyan gado,Nan dannan bacci ya dauke sa. ******** Junaid kam bayan ya shiga dakinsa,ya kasa kwanciya so yakeyi yaje yaga sultana amma baisan inda aka kaita ba,dan har clinic na gidan sai daya duba amma bai ganta ba,shi tsoronsa ma kar ace boss lion fitar da ita yayi a gidan,saidai kuma yasan wannan abune me wiya ya fitar da ita tunda uncle tareeq yaso yanuna masa isa,shikuma bazai taba yarda da hakan ba. Yanke shawara yayi zaije kawai ya samu ya Ashman ko yasan inda aka kai sultana,fita yayi daga daki ya wuce dakin yaya Ashman. Shiga yayi da sallama a bakinsa,bakowa a daki ,kashhh matawa yayi yanzu haka yana dakin gym ,komawa yayi ya wuce can dakin gym din a tsaye ya gansa da da karfe mai nauyi a hanun sa yana up and down da karfen, ganin junaid ya shigone yasa ya daina daga karfe ya samu wajen ajiye wa ya ajiye. Kamo hanun sa Ashman yayi suka zauna akan resting chair dake dakin yace”junaid kai da bakada lafiya me ya fito dakai ,daga daki,marairaicewa junaid yayi kaman zaiyi kuka irin yan da shagwababun yarannan suke yi yace”yaya ash na warke fah dama zuwa nayi na tambaye ka ina aka ajiye marar lafiyannan,dan na duba har clinic ban ganta ba. Ganin yanda junaid din ya damu ne yasa Ashman ce masa”muje ba nuna maka inda take,dan shi jiya yaga lokacin da “boss lion” ya dauke ta ya wuce da ita dakin,kuma bun ya bashi mamaki ba dan kadan ba,dan shima ya fitone dan yaga an dauke tane daga falon kokuwa ba a dauke ta ba. Gaba yayi shikuma junaid nayana binsa a baya ,har kuka isa plot 4 ,zaro ido junaid yayi yace”yaya ash dan Allah karka kaini wajan yaya boss wallahi zai batamun rai ne,dan shi harga Allah ya maida yaya boss ne yace a kira sa. Tsayawa ganinsa Ashman yayi dan junaid har yaso ya bashi dariya wallahi ganin yanda ya wani tsure,sai zazzare ido ya keyi. “Ba kai kace na kaika wajan wace ka buge ba?”gyada kai junaid yayi alamun eh”Toh ka kwantar da habkalinka wajan ta zan kaika,ka gane”eh junaid yace. Kofan dakin suka tsaya ,junaid ya juyo yana kallon yaya Ashman da mamaki dan shima bai taba shiga wannan dakin ba dan a kule yake kullum tunda suka zo gidannan. Shiga ciki sukayi dukansu biyu,Ashman ne ya kunna wutan dakin ,dan dakin da duhu,dan boss lion ya kashe wutan dakin kafun ya fita. A kwance take yanda boss lion ya fita ya barta,tananan yanda take ,bata ko motsa ba dan har yanzu bata dawo daga suman da tayi ba. 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 22 A kwance take yanda boss lion ya fita ya barta,tananan yanda take ,bata ko motsa ba dan har yanzu bata dawo daga suman da tayi ba. Shiga ciki sukayi ,wajan gadon,junaid yana ganin fuskanta ,ya zaro ido tare da dafe kirji,ya juya ya kalli Ashman yace”yaya Ash Allah yasa dai ba mutuwa tayi,kaga duk jikinta jini,wannan kam sai an kara mata jini inaga kafun ya far fado. Ashman kam ganinsa kawai yake yi yama rasa me zaice ma Ohoo,ganin yanda kan yarinyar ya bugu,dan taji ciwo sosai a kanta ,she fatansa ma kartayi loosing na memories nata . “Yaya ash ko zamu wanke mata fuskanta ne dan naga duk ya baci da jini,ba’a gane fuskanta fah. Wani kallo Ashman ya jefawa junaid irin na bakada hankalin nan yace”wai ni junaid ina ruwanka da ita ne kabar ta mana ,a yanda ka ganta,idan ta tashi ta wanke fuskan nata,idan haka wuce mu tafi dan bana son ,shishigi da shiga abunda bai shafe ka ba,kuma wallahi saura idan ta farka kace zaka shishige mata zaka sha mamaki dan a “boss lion “zan fadawa,dan naga ni kadai kake tsoro. Marairaice wa junaid yayi yace”yanzu yaya ash meye yayi zafi da zaka ce zaka fada wa yaya boss ,ni ba abunda zaina hada mu da ita har ta warke ta koma inda ta fito. “Good ,kwanda da kayi wa kanka karatun ta nutsu ,idan ba haka ba kuma kasan sauran ….. Wuce mutafi ,idan ya farka sai muzo mudu ba ta,”Toh junaid ya fada tare da bin bayan Ashman suka fita daga dakin kowa ya wuce dakinsa. ____________________________________________❤️ 8:10pm A hankali ya bude idonta da sukayi mata nauyi sosai,idonta sunyi dark blue ,saboda dadewan da sukayi a rufe ba tare da ta bude ba. Akan chandelier dakin ta fara gani sai take ganin abun kaman a mafarki ,dan yanda dakin yayi haske,abun gwanin sha’awa da kuma burgewa ,dakin ta fara bi da kallo, tana tunanin ko mutuwa tayi ne dan wallahi daki nan ba karamin haduwa yayi ba ,komai anjera shi yanda ya dace. Mikewa tayi daga kwancen da take,kanta yana mata wani irin ciwo da tunda aka haifeta bai taba mata ba,lokaci daya abunda ya faru ya dawo mata kai,firgita tayi,ta sauko daha kan gado ,tsoro ne da firgici ya kamata,ta fara tataba jikinta dan taji shin da gaske itace Kodai mutuwan tayi ne. Tabbass tasan ba mutuwa tayi ba,dan mutuwa tayi kuma ta ganta a aljanna tasan baza taji zafin ciwon da kanta yake mata ba,kuma gashi kayan dake jikinta lokaci da ta gudu daga gidan karuwai ne,wannan yana daya daga cikin abunda da yasa ta gane ba mutuwa tayi ba’toh amma ina take ‘waye ne ya kawota nan wajan. Futsari take ji amma ta kasa zuwa tayi,sai da taji ya kulle mata mara kafun ta sauka taje wanjan kofan da ta gani a cikin room din,bude wa tayi a hankali ,taja kafafunta da suke yi mata ciwo saboda buguwan da tayi,lokacin da junaid ya bugeta,Allah yaso ma bata karye ba kota gurde kawai kafan yayi tsami ne. Tana shiga ,sai data shaga da kallon bandakin,toilet ne daya amsa sunansa toilet,komai na ciki white color ne,wajan cupboard taje dan yi futsari,tana gamawa ta wuce wajan sink ,tajikin a kwai mirror,tana zuwa wajan kaman ance dago ki kalli mirror,batasan lokacin da ta sake ihuuuuuu mai karan gaske ba,ganin yanda fukanta ya baci da jini bazama ka gane color skin nata ba ,bandage na kanta ma ya sake baci da jini,abunda ya tsoratata kenan yasa tayi ihu ba tare da ta shirya ba. Tana gama ihuuu n taji kanta yana juyawa,idonta suka rufe,tayi baya zata fadi. Cikin sauri Ashman ya tare ta,tare da daukanta a kafadansa ,ya fita daga dakin ma gaba daya clinic ta wuce da ita,dan annan ne zata samu ishashe ne kulawa, tunani yake yi a zuciyansa “yanda yake mamakin wannan abun ,shi bai ma san meyasa “boss lion” kawota wannan dakin ba ,wata kila saboda mugunta ne yasa yayi hakan ,idan ba haka Taya zaka je ka ajiye marar lafiya ita kadai a daki ba tare da wanda zai kula da lafiyanta ba ,yasani yanzu haka da wata manufa yaya boss ya ajiye ta a dakin. Shima abunda yasa yaji ihuuun ta saboda,ya kaiwa boss lion coffee ne yana dawowa yaji karan Ihuuunata shiyasa yashiga dakin nata dan yaga akan wani dalili ne yasa zata wani yi musu ihuuu da daddaren Allah,sai kuma ya tarar bata cikin dakin,shi yasa ya yake shawaran shiga cikin toilet din,anan ya tarar da tana shifin faduwa. *** Daya daga cikin dakin clinic din mai kyau ya shiga ya kwantar da ita, wani sojane ya shigo da lab coat nashi tare da wiyansa lan kaye da stethoscope 🩺 alamun doctor ne. Yana ajiye ta ya fita domin samo mata kayan da zata saka koda kala biyar ne,idan yaso in taji sauki sai suje da junaid ya siya mata duk abun amfani. Doctor ne ya shiga dubata,tare da goge jinin dayake fuskanta tasss ya goge nan dannan haske ta ya fito,kafun ya warware bandage 🤕 din da ke kanta yayi dressing na wajan ,tare da saka mata sobon bandage a kannata ,kafun ya dauki blood pressure monitor dan duba yanda pressure ta yake,ai kuwa sai da yayi higher dan ta saka damuwa a ranta. Yana gamawa yayi mata x-ray a kanta dan duba yanda kanata yaje batan ya gama ya saka mata drip tare da yi mata alluran bacci ,nan da 3 hours zata tashi. Bayan ya gama mata abunda zaiyi ya fita ya bar dakin,tare da rufe kofan. After 30 minutes sai ga Ashman ya dawo tare da wani soja a bayansa hanunsa riqe da ledodi irin na boutique dinnan,yana ajiyewa ya fita ,shima Ashman din ,ganin ta juya baya,hakan yasa baiga fuskanta ba,shima ya fita daga dakin. ****** Boss lion kwance yake akan L-shape chair dake dakinsa idonsa a rufe kaman mai bacci amma baccin yakeyi ba,takaici kawai ya isheshi,dan wannan ihuuun da sultana tayi danshi a rayuwansa ya tsani hayaniya kwata kwata,ihuuu nata kuwa har cikin kokon kanta taji shi,shifa wallahi harya fara nadaman barinta da yayi ta zauna masa a gida. Tashi yayi ya wuce toilet yayi wanka,bayan ya fito ta wuce dressing room ya shirya cikin pajamas nevy blue masu kyau da tsada,kwanciya yayi dan shi bai cika samun lokaci yana yin bacci ba dan wani lokacin ma till down yake yi. Karan bude kofan dakinsa yaji anyi,amma saboda miskilanci ko kadan bai nuna alamun yasan da mutum a dakin ba,danshi komin kankantan motsi idan anyi yanaji,dan kwata kwata bashi da nauyi bacci,inashi ina dogon bacci,suda da suke zuwa yaki,any time ana iya kawo musu hari. Junaid tunda ya shigo yake dari dari dan yansa yayi lafi amma dole ya bada hakuri,cikin dauriya ya haye kan gadon boss lion ,ya rungumesa ta baya,yace”please yaya kayi hakuri,wallahi bada sanina na bugeta ba,kawai ganinta nayi a gabana,kuma kasan bawa baya taba kaucewa kaddararsa,duk inda kake sai kaje ka same ta,please yaya am so sorry it’s me your junior,please don’t be angry with,bazan kara fita ban fada maka ba,shima banyi tunanin zaka dawo ka samu bandawo ba,please and please my yaya . Boss lion yana jinsa amma ko uffan bai ce masa ba yanda kasan ba’ayi ruwansa a dakin ba,tsabar miskilanci. Ganin bai kulasa bane yasa ya fashe da kuka harda shesheka,dan yasan idan ba kukan ya masa ba dakyar ya kulasa,dan kwata kwata bayasan ganin kukan su. Kukan da yake yi ne ya karyawa boss lion zuciya dan bayaso ganin kukan yan uwansa,wannan Alkawari ya daukawa kasa nace wa bazai bari suyi kukan maraici ba. Jawo sa yayi jikisa yana bubuga bayansa alamun rarrashi ,duk da haka bai ce dashi komai ba,nan take junaid yayi shiru a jikin boss lion sai shakan dadda dan turaren jikin boss lion yake kamshi sai tashi yakeyi,tuni ya soma ajiyan zuciya akai akai ,Chan bayan 5mins dikinsa ya saki ,alamun bacci ne ya daukesa. Tsayawa yayi yana kallon kyakyawan fuskan junaid dake sauke numfashi a hankali a hankali,abubuwa dayawa suna masa yawo a kai,janyo musu blanket din yayi ya rufe su , tare da yi addu’a ya fasha fa musu gaba daya,shima bai jima ba bacci ya dauke sa . Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 page 📃 23 *** Sultana tun bayan bari doctor da ashma ,ba wanda ya sake dawowa dakin,after 3 hours ta tashi ,bata jin wani hajijiya,sai dan ciwon kan da ba’a rasa ba,shima saboda buğulan da kanta yayi ne. Kasa bude idonta tayi dan ji takeyi kaman an like matasu da gum,haka dai doctor yashigo ,ganin hanunta yana motsi ne ya tabbarar masa da ta tashi ,amma tasan bazata ita bude idonta ba,dan haka kawai ya koma yasa gobe insha Allah,idonta zai bude. Sultana kam jin ta kasa bude idonta ne ,yasa ta fara tunanin ko dai ta makance ne,a haka har wani baccin ya sake dauketa ,tsakar dare. WASHE GARI😌 A hankali ya bude idonta ,abunda ya fara dawomata shine Toh dama ba makan cewa rayi bane. Tashi tayi ta zauna tana kare sa dakin kallo ,kallon dakin takeyi,da mamaki dan tasan dai ba a nan dazu ta gantaba,Tuna a bandaki take ne yasa tayi saurin taba fuskanta dan taji shin har yanzu da jinine ko kuma A’a. Jin abu komai a fuskanta ne yasa ta sauke ajiyar zuciya,tana zaune sai ga doctor ya shigo ,ya isa inda take yace”how are you and how is your body,a hankali muryan marasa lafiya tace,Alhamdulillah”I hope you are feeling better?”gyada masa kai tayi kawai. Mika mata ledan da Ashman ya kawo mata yayi yace”ga kayan nan ki shiga kiyi wanka,ko zakiji dadi jikin ki”ok tace,daganan bata sake cewa dashi uppan ba.shima fita yay dan ya bata waje ta shirya,yana fita ta soma maganan zuci “ina nake ne yanzu,Allah yasa ba masu cutar wa bane,duk da dai bata ga alamun hakan ba,amma fuskan doctor a tamke yake ,kaman na ogansu dan basa daukan wargi. (Karku manta duk maganan nan da English suke yi ,dan ita tayi school zu jss 3 ta tsaya ) Tashi tayi ,ta nufi toilet tana tafiya a hankali kaman wace kwai ya fashe a ciki,shiga tayi da ledan a hanunta tana budewa taga ,abayas kala biyar masu shegen tsada da kyau,stones din jiki sai shining suke yi,ga packeds na pants,bra,lotion,perfumes,lipstick , towel,sai takalmi guda biyu daya na yawo a cikin daki daya kuma na kwalliya. (Karkuyi tunanin Ashman ne ya je yasiyo mata A’a ,saika wani soldier yayi yaje ya siyo,bayan ya siyo ne ya kawo masa,batare da ya duba ba,ya kawo mata cikin dakin) Wanka tayi,mai kyau ta wanke duk wani datti dake jikin ta ,ta shafa lotion din sannan ta saka su pant,bra, duk da dai duk sun mata kadan da ta fah sultana,Allah ya albarka ce ta da dukiyan fulani ,gasu a tsaye suke churrrr,ga hips hmmm ba’a magana Coca Cola body ,kuke ji,ta daura abayanta akai ,gashinta data wanke ,ta dauki towel din ta tsame ruwan jiki ka fun ta yafa dan kawalin abayan,tayi kyau ta fito a asalin balarabiyar ta ,sai dai muce Tabarakallah Masha Allah,duk da ba tayi kwalliya ba amma fuskanta ba karamin kyau yayi ba kaman ,iya lipsticks kawai ta shafa. Ta koma kan gado ta kwanta amma ba bacci take yi ba. ________________________________________🥰 Junaid kam tunda sukayi sallan asuba,ya koma dakinsa ,yay wanka a bunsa cikin ,black jeans with white t-shirt sunyi masa kyau ,abunku da ma tashi sai yalki yakeyi,ga gashinsan nan ya sha gyara abunsa. Fitowa yayi daga part nasu direct clinic ya wuce,dan sunyi magana da Ashman ya fada masa an maidata clinic. Yana shiga ,sojojin da suke wajan suka nuna masa inda dakin sultanan yake,da sallama a bakinsa ya shigo cikin dakin,yanda taje Dazu haka yashigo ya sameta,kanta hade da jikin gadon ,zama yayi a kujerun dake ,kusa da ita,kuma har lokacin bata dago taga wayene ya shigo ba,dan ita a tunanin ta doctor ne ya sake shigo wa. Yakai 4minutes ba Wanda yacewa kowa komai,sai can junaid yayi gyaran murya “how are you ,how was your body”sai a lokacin jiyo ta kalli junaid ,batasan lokacin da ta hadiye Yawun dole ba dan ba Karamin kyau ne da junaid ba ,sai dai Masha Allah,kasa magana tayi,ganin ya kasa magana ne yasa yace”kiyi hakuri ,bada sanina na burgeki ba,bansan kina wajan ba da bazan burgeki ba,and Allah ne ya kaddara haka zai faru,kuma bamuda ikon sauyawa. Ajiyar zuciya ta sauke dan sai lokaci ta gane wayanda suka burgeta ne suka kawota ,inda take yanzu. “Karka damu ,bakai ya kamata ka bada hakuri ba ,nine yakamta na baka hakuri dan ni nashiga gaban ka da gudu. Junaid fah tunda ta dago ta kallesa ,ya shagala da kallonta dan sultana badai kyau ba,shifa baiyi tunanin yarinya bace ,dan a tunanin sa ma wata 28 ne dan sai yanzu yaga fuskanta mai kyau. “It’s ok,then can we be friends,cause your beautiful,omg ,amma fah baki fi yaya boss kyau ba dan shi ,first class ne indai wajan kyau ne,ko kafansa baki kai ba yarinya,ya fada cikin tsokana,jin ya ambaci yaya boss sai da zuciyanta ya tsinke bata san meye saba,wayin cewa tayi. Murmushi tayi tace”gaskiya baka da wata matsala Kanada kirki sosai,kuma ai kaima ka fini kyau sosai”haba yarinya ai ko makaho yasha fa fuskanki da nawa zai gane waye yafi kyau. “Meye sunan kanwar tawa?,murmushi tayi mai sanyi tace Sultana,”wow nice name,ni zan ina kiranki da sis sultee,haka yayi miki ko A’a acanja “cikin jin kunya tace hakan ma yayi. Dariya yayi yace”Toh ni bazaki tambaye sunana ba kenan ya fada cikin shagwaba,me sultana zatayi idan ba dariya ba tace”gaskiya shagwaba tayi maka yawa,Shikkenan meye sunan ka,”sai da kika gama jamun aji tukun zaki tambaye ni,zan fada miki badan halinki ba”my name is junaid”ok me too I will be calling you with yaya junaid,because you my elder brother,is it ok for you”yeah I really appreciate it,kinga nima yanzu nayi kanwa. Toh yanzu dai ba wannan ba ,ki fada mun idan akwai abunda kike bukata sai na kawo ma my sis sultee ,”wani farrr da ido sultana tayi irin ya fasa mata kanan,ta shagwabe fuska irin na tabararun yaranan ,duk da bata masan ta iya ba tace”yaya junaid yunwa nake ji sosai ,”ohh Allah sarki sis karki damu yanzu zankawo miki abinci kin ji ki bani nanda 5 minutes yanzu zan dawo. Bai wuce 6 minutes ba sai gashi ya dawo hanunsa dauke da basket 🧺 da abinci a ciki,shida kansa yayi saving nata ,chicken pepper,with potatoes chips,da kuma wani abincin su irin na turawa,masu ruwa ruwa,daura plate din yayi akan bed side drawer,a kwai table a wajan ya ajiye ye mata. Sultana kam banda kallansa ba abunda take yi,ganin yanda bai Santa ba saisan daga ina take ba amma har yake kiranta da sister nashi,kuma ya kula da ita abun ba karamin farin ciki ya sata ba har idanunta sun ciko da hawaye amma bata bari sun zuboba ta shanye abunta. Sakko wa tayi tana cin abinci junaid sai tsokanan ta yake yi abun gwanin burgewa,Masha Allah. 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 Book 1 Last page 📃 24 USA 🇺🇸 AFTER 4 DAYS 💞 Jikin sultana yayi sauki sosai ta warke garau kaman ba ita ba , sai abunda ba’a rasa ba,gashi ya Kara wani haske skin nata ya murje,saboda hutun da ya samu,bata aikin komai sai na wanka,sai zaman cin abinci,Shikkenan abunda take yi. Junaid da Ashman kullum sai sunzo sun dubata duk dadai Ashman bai wani bata fuska sosai ba,amma ta tafi dashi,dan lokacin daya fara ganin ta ya girgiza da kyau ta dan ba kasafai ake samun irinsu ba,amma duk da haka yana jajja aji,da farkoma da sultana ta gansa ta tsorata gashi shima jibgege,duk da baikai “boss lion” ba amma dai shima irin ingarman namiji ne gashi kyakyawa sosai ,dan yafi junaid kyau,amma junaid maga kyakyawa ne . Yau aka maidata chan dakinta,tabar zaman clinic,dadi take ji takoma chan cikin gida,sai dai kuma tana tsoron haduwa da “boss lion” dan junaid ya bata labarinsa amma kadan ba sosai ba,dan yawanci yabonsa yakeyi ,kawai dai yace mata ,wallahi tabi a hankali kartayi abunda zai jawo hankalin boss lion dan abun bazai musu kyau ba,abunda take ma fargaba kenan “gashi doctor yace buguwan da tayi akai zai na sakata yawan suma idan abun ya firgitata ko ya bata tsoro,amma dai an daura ta akan magani. Zaune take a gefen gado ,tana ta tunanin rayuwa,taji anan knocking tace”yes come in” junaid ne ya shigo jikinsa sanye da white trousers with red t-shirt fuskansa sanye da face marks,ka fansa sanye da sneakers red masu kyau da tsada ba karamin kyau yayi ba abunku da farin fata sai yalki yake yi,abunsa ,gashinsa ma yasha gyara ,yasha mai kala kala ya kwanta luf luf,abunku da gashin turawa. Shigowa yayi ya isa har inda take,dan tunda yashigo wankansa ya tafi da ita ,ta wani kafe shi da ido,dan ba karya yayi kyau ,hura mata iska yayi kan fuska,sai a lokacin ta gane me tayi,kunyane ya kamata,ta su kıyar da kanta kasa tana murmushi mai daukan hankali,”ya kika kalle ni nayi miki kyau ne,dan kinsan yayan naki badai farin jinin yan mata bah,”galla masa harara tayi cikin wasa tace”waya fada maka kai nake gani tab “gwanda ma kasake chanja wani kaga dan wannan banda muni ba abunda ya Kara maka,ta fada tare da kashe masa ido daya. Bata fuska junaid yayi jin wai baiyi kyau ba “please sis sultee wai da gaske banyi kyau ba,”ya fada tare da dan damuwa akan fuskansa , dan shi a ganinsa yayi kyau”Haba”yaya junaid kayi kyau dan harkafi kyau kyau ma ,na fada maka,waya isa yaga handsome brother na haka yace baiyi kyau ba saidai kishi yake yi,cikin jinin dadin ta yabi kwaliyansa yace”da gaske nayi kyau ?”gyada masa kai tayi alamun eh. Oops na mata ma zuwa dama nayi na fada miki akan ki shirya zamu fita anguwa,kuma kiyi sauri karki batamun lokacin ina jiranki a main falo,dan banason Africa time,kinji ko nanda 7 minutes ki fito,ya fada tare da fita gaba daya daga falon. Tashi tayi ,ta canja kaya ,dan bata wuce 30 minutes dayin wanka ba,abaya ya dauko black color yasha stone ta dauki black plat shoe,ta saka tayi rolling na gyale abayan,ta shafa lipstick ,tayi kyau ,dan kana ganinta kaga balarabiyadan shigansu tayi,ba karamin kyau Abayan ya mata ba,ta fito ta wuce main falon gidan. A falo ta samesa tare da uncle Ibrahim,da uncle tareeq,har kasa ta tsuguna ta gaishe su,uncle tareeq ne kawai ya amma mata cikin sakin fuska har yana tambayanta ya jiki amma banda uncle Ibrahim da yayi cikin cikin da fuska,sai faman Shan kamshi yake yi Dan ba bakin magana,dan yasan indai yayi wani abun,ba abunda zaisa junaid baije ya fadawa “boss lion” ba,shifa har junaid din yake jin haushi,kaman yayi yaya ,sallama suka musu tare da ficewa daga falon. Tunda suka fito take makale a jikin junaid dan wallahi bala’in tsoron sojoji take yi ,shiyasa dazu da suka fito daga clinic taga sojoji sai kace a Barack ga gidan kirarre sai kace ba’a duniya mutum yake ba,wayannan abu biyun ba karamin girgizata a lokacin sukayi ba,a take jikinta ya fara rawa har take tambayan junaid”yaya junaid Anya ku ba yan yankan kai bane,sai hawaye sharrr” dariya junaid yayi yace”Haba sis sultee kincika tsoro dayawa,kina tunanin damun yan yankan kai ne,zaki kai har yanzu a raye ne?”common ki goge hawayen ki idan ba haka ba kuma ,saina hada ki da lucky ,ya miki dan banzan duka dan yau aka dawo dashi gidan” ki kwantar da hankalinki ba abunda zai same ki na miki Alkawari kinji,ko baki yarda da brother ki bane”girgiza kai tayi alamun ta yarda,yace”to karki yarda ki shiga sabgansu,ko a hanya kuka hadu dasu kice dasu komai kiji”Toh tace dan sai lokacin taji dan relief kadan,amma hakan ba yana nufin ta daina jin tsoron su bane A’a, dan ko 1% bai raguwa,har tana cewa Allah yasa karta sake fita waje,sai gashi har ko 3hours bata yiba ta sake fitowa,haka ta dunga bin gidan da kallo ,tana nuna kwauyan cinta a fila,ko a jikinta. Wajan wani understand ground suka shiga,motocine masu bala’in yawa ,dan zasukai 100 and some things,gasu gabada ba ,baya a cikin motocin, kana ganinsu kaga dollars tayi kuka a cikinta ,rolls-Royce boat tail ,Bugatti cantodieci ,bugatti la voiture noire,Bugatti divo,etc motocine masu daukan hankali,Wanda idan bakada cikar imani,zai shagaltar dakai a duniya ka ke. Wajan Mercedes benz suka shiga red color mai tsadan gaske,junaid be da kansa ya saka mata seatbelt din Dan ba’iya sakawa tayi ba,yaja motan suka nufi first get a hakan ma sunyi tafiya mai tsayi kafun suka iso first get ,akayi screening na plate number su kafun aka basu go ahead na tafiya,sultana kam ba abunda takeyi sai kalle kalle,tafiya sukayi mai dan tsayi kafun suka iso wani narkeken mall ,dan ubansu,daya gaji da haduwa ta ko ina , dan up stairs ya kai kusan 8 . Shiga sukayi basu tarar da mutane sosai ba,tunda suka shigo wajan jikin sultana yayi sanyi,junaid ne yace”muje ki zaba duk kalan abunda yayi miki kinji sis sultee,idonta cikowa yayi da hawaye ,cikin sauri ta maidasa,tare dayima junaid murmushi kawai amma ta kasa magana dan tasan tana magana zata iyayin kuka. Sultana kam kasa daukan komai tayi junaid ne ya dings kwasan duk abunda yasan zai mata kyau kawai yake yi,t-shirt 24,jeans 12, skit 12,abaya 30,normal gown 25,sweaters 12,tops 12,shoes 24 both plat and hill,bag 24 both school bag and fashion bag, socks 24,hand gloves 12,earrings 24,ring 24,pendant 24,bras 2pack,pants 2packs,make up kit,lotions,perfumes,pads etc duk abunda yasan zata bukata sai daya dauka mata ishashe ,kafun suka wuce wajan biyan kudi. Sultana kam tunda taga yana ta jidan kaya tasawa ranta cewa wata kila a kanwarsa yake siya mawa,duk dadai bai taba mata zancen wata ba. Black card ya ciro ya badu su ,uncountable dan ko nawa zaka cire bazai kare ba,a wajan “boss lion” ya karba yace mishi zaije yayi shopping ne,ana yi musu total,suka karbi black card din suka cire milions of dollars,daukan kayan akayi aka saka masa su,a cikin motan sojojin dake gadin sa,yaja hanun sultana suka shiga mota,dan kanta har ciwo ya fara mata,gashi har wani hajijiya take ji,shiga cikin mota sukayi suka wuce gida ba Wanda yacewa kowa komai,sai da suka sauka har zata wuce,yace “sis sultee muje mu kwashe kayan dan kinsa ba barinsu akeyi suna zuwa part na yaya boss ba,gashi kekuma can aka wulla ki,ya karasa maganan yana murmushi. Sultana kam tunda taji cewa wannan duk kayantane batasan lokacin da kuka mai ratsa zuciya ya kubce mata ba ,”hey sis what happen naga kina kuka kodai kayane basu miki ba a canja wasu,”Girgiza Kanta tayi cikin kuka tace”yaya junaid wallahi Allah bansan da wani baki zanyi muku godiya,nagode,nagode yaya junaid Allah ya saka muku da gidan Allah,Allah ya kara muku budi,kaman yanda kuka karantamun rai,Allah ya faranta muku ninkin sa,”bata fuska junaid yayi”wai mesa kike mun godiya,kifah kanwa tace kin cancanci fiye da haka ma dan haka indai kina so mu shirya to karki sake mun godiya kinji ko”gyada masa kai tayi tana goge hawayen daya sakko mata,haka suka kwashi kayan suka wuce wajan lifter shiga suka yi dukansu biyu. After some seconds sai ya bude,yana budewa ba tare da taduba ba kawai ya saka kai,jikake dummmmm ta buge kirjin “boss lion”da zuwansa kenan zai shiga lifter . Ran “lion tuni ya baci ganin yanda mace take kwance akan faffadan kirjin sa,cikin sauri junaid ya kamo hanun sultana zai matsar da ita daga jikin yaya boss dan tunda sultana ta fada jikin boss lion ya saki kayan dake hanunsa jikin sa har rawa yakeyi dan yayi mungun tsorata da ganin yanayin yanda fuskan boss lion ya baci. Sai dai kafun yaga ma janta daga jikin yaya boss”tuni yaya boss ya sauke mata mari a fuska ji kake tassssssssssss hakan ma ba duka hanun sa bane ya sauka akan fuskanta ba. Allah sarki sultana ita batasan ya akayi ba kawai ji tayi ta fadi a jikin mutum ,ga wani fitinane kashi mai sanyaya zuciya daya bugi hancin ta yasa ,ta sake kwanciya tayi luf a faffadan kirjinsa ,sai kuma taji junaid ya ja hanunta kafun ya ankara kawai taji saukan mari daga sama ,unexpected,ji tayi kafafunta sun gagara daukanta,idanunta sun rufe ruf,tuni ta sume a jikin junaid,dan shima yasan bakaramin maruwa tayi ba a hanun “boss lion” Anya sultana zata iya rayuwa a wannan gidan kuwa ? Shine boss lion zai rage zafin ranan nashi ne idan har ya fada soyayya ? Ya labarin su innah a gombe? Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋 SIRRIN DAKE BOYE _*❤️ ( The hidden secret 🌹) 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ 🌍 Destiny,Love ❤️& Romance 💋 2024/2025🔥 Written by AMID ✍️ Bismillah Rahmani Raheem Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 Page 📃 25 Junaid yana riqe da hanunta daya ,dayan hanun kuma ya janyo ledodin dake bakin kofan lifter. Shiga cikin lifters “boss lion “yayi batare daya sake kallon inda su junaid da sultana suke ba,dashi ko za’a daura masa gun a kansa bazai iya cewa ga yanda sultana take ba,shi dai kawai yaji mutum a jikinsa kuma da kayan mata,shiyasa kawai ya chass keta da mari,shiga yayi ya wuce ya bar junaid rike da sultana. Ganin “boss lion”ya tafi ne yasa junaid din sauke ajiyan zuciya,kafun ya saka hanun sa duka biyu ya dauke ya direct dakin ta ya wuce da ita ya kwantar da ita akan gado,ya tsaya yana ganin fuskanta da yayi jaa,ga shatin yasun yaya boss akan fuskanta ,ba karamin tausayi ta bashi ba,dan yasan koshi aka mawa wannan Marin sai haka. Dakinsa ya wuce ya dauko maganin da zai shafa mata a fuska,suka hadu da yaya Ashman ,Annan yake sanar masa da cewa yaya boss ya mari sultana,jin hakan yasa Ashman cewa”muje na duba ta naga fuskan nata,tare suka wuce dakin,lokacin da Ashman yaga yanda fuskanta harya kumbura sai daya tausaya mata,shi karan kansa ya sani ,duk wanda yasha Marin boss lion Toh akwai matsala. Junaid ne ya shafa mata maganin a fuskanta,har zasu tafi sai kuma yaya Ashman yace”amma dai ba haka zamu tafi mu barta baka shafa mata ruwa ba,aaa ya Ashman wani shafa ruwa kuma,bayan tayi bacci ,yanzu sai kawai ana zaman lafiya,ince zan shafa mata ruwa,ai sai ta iya Hajja ce wa ma,kallon bakada hankali Ashman yayima junaid” junaid nikam ka koma shaye-shayen ne bamu sani ba”bata rai junaid yayi yace”yanzu tsakani da Allah nayi maka kama da wanda yake shaye-shaye,”yeah tunda ,kana ganin mutum a sume amma kana cewa bacci take yi,ko kuma dai so kakeyi daga suman sai ta wuce can,” Zare ido junaid yayi yace “wani can zata wuce,kaikam ya Ashman kana fadan Alkhairi mana kokayı shiru,naji yanzu zan sha fa mata ruwan kafun bakinka ya kamata,ya fada da sauri ya shiga toilet ya ibo ruwa a cup ya matso wajan sultana,a hankali ya shafa mata ruwan akan fuskanta ,shiru bata motsa ba,ya sake shafa mata shima shiru bata motsa ba,kawai sai junaid ya fashe da kuka”yanzu ya Ashman meye amfanin irin wannan maganan da kayi,yanzu kasa bakinta ya bita,Shikkenan fah ta rasu,wayyo Allah na shiga uku ba,wayyyo Allah na shiga uku na ,ya Ashman ka cuceni wallahi,Shikkenan one and only sister na ta ,tafi ta barni,wallahi bansan haka mutuwa take da zafi ba,amma dai yaya boss ya cuceni ya kashe mun ita,gaskiya sai Allah yasaka mata,sai munyi shari’a daku,baiwar Allah bataji ba bata gani ba ankashe ta ,kuka yake yi bilhaki yana sumbatu,shikaran kansa ka tambayesa meyace bai sani ba. Me Ashman zaiyi idan ba dariya ba,dan wallahi yanda junaid yake ta zaginsu yana kuka,ba karamin dariya ya bashi ba ,sai da yayi dariya mai isansa,daya dade bai yi ba ,ya matso wajan junaid ya marairaice fuskan yace”haba junaid sai kace bakasan kaddara ba,lokacin tane yayi , shiyasa ta tafi,dama Allah yayi ita bamai nisan kwana bace,”tabdijam sai wallahi ba zaku kashe ya a banza ba ,saina dauka mata fansa,sai wani hawayen sharrr. In serious face ,Sake dafa ka fadan junaid yayi yace haba junaid sai kace marar wayo wa yace maka mutuwa tayi kai da kanka fa kace ya mutu,ganin babu alamun wasa a maganansa ne yasa junaid goge hawayensa yace da gaske bata mutu ba”gyada masa kai ashman yayi”Toh ai kaine ka kasa nutsuwa ka gane cewa tun ruwan farko daka shafa mata ta farfado,dan yasun hanunta sun dan motsa sai kuma bacci ya dauke ta,kazo ka wani sani a gaba kana ta mun kuka har dacewa saika dauka mata fansa,kan abunda muka mata,kenan sawa zakayi a daure yaya boss ni kuma a kaini magarkama ko,ai kaman a kunen yaya boss cewa ka fifita bare akan sa. Ai ba shiri wasu sabin hawayen suka fara zobowa junaid jin za’a fadawa yaya boss abunda ya fada ,kuma bai masan ya fada hakan ba”wai yanzu yaya Ashman saika fada masa ?,haba dan Allah nifah wallahi ban masan na fada hakan ba ,dan Allah karka fada masa ,kayi hakuri subutan baki,amma banmasan na fada hakan ba,kaji please ya Ashman dina. Uhmmm junaid har dayimun dadin baki kuma yanzu,ba dazun nan ka gama zagi na ba ko ba haka ba”Toh ai na baka hakuri ko,Toh Shikkenan na hakura amma duk lokacin da ka kuskura ka sake irin wannan maganan ba zata tsaya iya muka dai ba,kaji ko’eh insha Allah ma bazan sake ba,”Allah yasa. Tashi mu tafi ,ka barta tayi bacci ko zata samu relief din abunda yake damun ta ,tashi junaid yayi salun alun suka fita daga dakin tare da kashi mata ruta,suka rufe kofan. Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍ ️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE❤️_* ( The hidden secret 🌹) Page 📃 26 🦋🦋🦋🦋🦋🦋 9:30pm in USA 🇺🇸 Zaune yake a gefen gadonsa,jikinsa sanye da boxers amma bai damesa sosai ba ,singlet ne a jikinsa duk da kuwa sanyin da akeyi,coffee ne a gabansa ,yana aiki a cikin system,hankalinsa gaba daya yanakan system din danabu yakeyi mai muhimmanci. Kaman daga sama ya fara jin ihun sultana,ciki gaba da abunda yake yi yayi,duk da kuwa bayason hayaniya kwata kwata,amma kam wanda ake kara wa ihu dan ihu takeyi tsakani da Allah,cikin bacin rai ya mike dan yasan junaid da Ashman basanan,gashi shikuma basan hayaniya . Mike wa yayi ya fara tafiya anutse ga jikinsan a murde irin na wanda yayi gym harya gaji,dansen hanunsa ma kadai abun kallo ne,cikin tayiyan kasaita ya wuce dakin daya San zai ganta ,dan ya sawa ransa sai yaci uban yarinyar nan kafun zasu daidai ta. Yana zuwa ya shiga cikin dakin babu excuse,a kwance ya sameta ta dukun kunu a cikin bargo jikinta sai kar karwa yake yi dan tunda ta tashi ta tuno abunda ya faru ta tsorata har ta fita a hayacin,ga radadain da fuskanta yake mata,kaman an kona fuskan takeji saboda radadi ,dan ba wanda zaisha marin boss lion ya tashi zamm wannan karyane. Matsowa yayi jikin gadon dan cikin kaniyanta,yaye bargon yayi ,hanu yakai zai sake wanke ta da mari aganinsa wanda yayi mata dazu bai isheta bane. Har yakai zai mareta sai a lokacin ya fara ganin fuskanta duk da marin da tasha hakan bai hana ganin kyakyawan fuskanta ba,ga shatin marin da yayi mata ya kum bura fuskan ,lips nata sai kyarma yake yi gashi yayi wani irin dark pink dinan,wanda duk wani lafiyayen namiji,dakyar idan sha’awansa bata motsa ba. Duk kallonan within some seconds ya mata ya dauke kansa,jiyayi bazai iya yi mata abunda yayi niya ,duk dadai shi karan kansa yayi mamakin haka,danshi ba ruwansa duk wanda yayi masa laifi hukuntasa yakeyi. Sultana kam tunda ya yaye mata bargo,ta kasa daga kanta dan gani takeyi kaman sake dukanta sa’ayi koma wanene,dan ba karamin tsorata tayi ba,inda wata ce ma sai ta iya haukace wama,idonta a rufe yake ruf . Dressing mirror chair ya janyo ya ajiye a gabanta ,ya zauna tare da yin crossing na legs nashi,kafun ya dubeta cikin kara hade fuska yace”hey open your eyes before I give you another slap,jin hakan ba karamin tayar wa sultana hankali yayi ba jin muryan mutumin dazu daya mare ta ,jikinta har rawa yake yi wajan tashi dan bata kaunan ya sake mata wani dukan,zama tayi taga yin da yake zaune ba wani rata sosai a tsakanin su . Dagowa tayi a hankali gudun kar tayi laifi,kalonsa tayi da blue eyes nata masu daukan hankali,zuciyanta sai daya bada wani irin dummm,dummmm,dummmm,gani kyakyawa mutum a gabanta da zata iya cewa tunda aka haifeta bata taba ganin kyakyawa irinsa ba,batasan ta shagala da ganin ba,har ta mantama da cewa shine ya mareta. Gyaran murya yayi”ganin yanda ta wani kafe sa da ido sai kace mayya,”idan na sake kamaki kina ganina saina cire miki idanu,ki bari na sake ganin kina kallo na ki gani,idan bakisha mamaki ba,numfashi yaja dan wallahi daure wa kawai yayi yake mata magana,dan miskilancin bazai barsa ba. “ sannan nan ba gidan mahaukata bane ,idan ke mahaukaciya ce Toh tun wuri ki fada mana mukai ki gidan mahaukata,idan ba haukaba kawai kisa mutane a gaba kin ihu,last warning nake baki ,kuma kakı sake bari ko a hanyane mu hadu ranki zai baci,mikewa yayi ya fice daga daki. Sultana kam ganinsa ba karamin tafiya yayi da imanin ta ba ,yanda ta gansan nan,tanajin ko kashe ta zaiyi sai ta kalle sa,ji tayi ma duk haushi marinta da yayi ya tafi,idan ya tuna kyakyawan fuskansa sai tayi murmushi,dan ba karamin burgeta yayi ba. A haka ya dawo ya sameta ,a yanda take,zama yayi akan kujeran tare da Mika mata maganin da zata shafa a fuskanta,hanunta har kyarma yakeyi wajan karba ,ko kallon nasa ma ta kasa tsayawa tayi Dan mugun kwarjinine dashi na bala’i ,bude murfin roban tayi ,dan ta gane maganin meye ne ajiki akwai hotan dake nuna nakuburin waje ko radadin ciwo,shafawa tayi a hankali ta kasa dagowa ta kalesa,damashi kam boss lion amfani yakeyi da wayansa,dan tun kallon farko da yayi mata bai sake ba,dan wannan ba halinsa bane. Tana gama shafawa ta mika masa roban,amma sai taga bai karba bama,ganin bai kulata bane yasa ta dago da idonta a hankali irin na munafukan nan ya kalesa,sai alokacin ya jiyo hada ido ,harara ya wulla mata tare da sake tamke fuskansa kaman an aiko Masada sakon mutuwa “ba tareda yace mata uppan ba dan yan miskilancin sun matso ,fice wa yayi daga daki zuciyansa nayi masa zafi dan ganin yake yi wannan abun da ta masa ma ai rainine dan haka gobe,saita bar masa gidansa tunda ba tare suka siya ba. Lumshe idonta tayi tana shakan daddadan turaren dakesa mutum ko ransa ya baci indai ya shaka to wannan perfume din to tuni hankalinsa zai kwanta ,dan ko Ina na dakin kamshin turarensa yakeyi kaman anan ya fesa. Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE❤️_* ( The hidden secret 🌹) Page 27 ________________________________________✍️ Kwance take a falo,jikinta sanye da dogon riga yar kanti peach color mai design na roses a jiki kanta sanye da peach veil bakaramin kyau kayan ya mata ba daidai jikinta ,fuskanta ba wani kwaliya tayi ba power,kwalli,dakuma lipsticks,ga gashin tanan yasha gyara , ta gaban kaman wanda ta saka jel ,sai dai muce Tabarakallah Masha Allah,dan Allah yayi halita,junaid ne da kansa ya nuna mata yanda ake amfanin da abubuwan da suka siyo,bayan yayi mata ya jiki,kuma yayi mamaki ganin fuskanta ,ba kumburin dayayi jiya ,fuskanta fess kaman ba jiya tasha mazga ba,dan maganin da tasha ,sha yanzu mafani yanzu. Zaman dakin ne ya isheta shiyasa ta dawo falo bayan ta gama break fast,bakowa dan duk kowa ya kama harkan gabansa, junaid ya tafi school amma tasan yanzu haka ya kusan dawowa shiyake ibe mata kewa,mikewa tayi da sauri tuno da maganin da ya bata,tabass kaman bata ganshi,a zuciyanta tace”tab yau na shiga uku agun mugun mutumin nan gwanda na shi naje naduba tukafu ya karyani a gidan nan,da gudu ta nufi elevator ta dan hawa na hudu ,sai kuwa ya budu,kawai shege wa tayi da sauri ,hankalinta ma baya jikinta jikawai tayi ta bugu da mutum. Tariga da tasan wata buge ,ai take jikinta ya fara rawa ganin yanda ta bugesa,kuma ta buge wayansa,a kasa ,dagowa tayi ta kallesa kaman munafuka,saikuma taga ba’ita yake kallo ba wayan data buge masa yake kallo,dan jira yakeyi yaga zata mika masa kokuwa ciga da ganinsa zatayi”hanunta rawa yake yi kaman a jona mata igiyan lantarki ,mika masa wayan tayi yiyayi kaman baisan tanayi ba ,sai kuma can ya dago idansa ya kali yawan ,ba abunda ya sameta dan ba normal waya bace irinta kowa ,musaman ya bada a company aka masa ,ba wanda yake rike irinta,kuma shi kadai zai iya sarrafata. Hanuntan yabi da kallo ganin yanda suke kerma ga kanta a sunkuye sai ruwan hawaye takeyi babu kakkaugawa,karban wayansa yayi a zuciyansa ya”ahh yarinya dakin bar kukannan kin tanada sa a inda zaifi miki amfani dan wallahi babu abunda zai hana yau bai hukuntata ba,shifa wani lokaci har mamamakin tsoronta yakeyi,mutum abu kadan tsorata kam farar kura,sake tamke fuskansa yayi sosai ,yanufi hanyan fita tare da cewa “ki biyoni,iya abunda ya iya fada kenan,jin hakan ne yasa sultana sake fashe wa da kuka dan wallahi kana ganin sa kasan ba wasa a maganan nan ubanta zaici. Sum sum tabi bayansa ta koma main falon kan wani hadaden kujera ya zauna da ba wanda ya isa yazauna idan bashi ba yayi crossing na legs nashi ko ina fess fess a gyare sai kamshi yakeyi,”acan kasan cafet ta yi Neil down,shiru kusan 10 minute bai ce da ita komai ba ,sai daya bushe iska dan kanshi kafun kafun yace” up and down zakiya babu adadi, harsai idan nice nace ya isa idan kika kuskura kika tsaya zangani,a duk inda nake,so warn your self,one single mistake…..I will kill the hell out of you, so start right now”da sauri ta mike ta fara yin,guda biyar tayi sai da taji kafanta sun fara rikewa dan ba irin wannan wahalan ta saba ba,ta cikin ye taji haushi kare a bayan ta. Nandanan jikin ta ya fara rawa fiye da nada dan wallahi ba karamin tsoran kare takeyi ba ,ganin wani zudumeme kare tayi irina turawa katı dashi ga gashi sosai a jikinsa yanda kasan karen brolers haka yake,irin ne wayanda akayi musu training sosai ,ba abunda zaka ce su musu baza suyi ba,wajan boss lion yaje ya fada jikinsa yanata tsale alamun yaji dadin haduwa da boss lion dan da kullum suna tare wani lokacin ma tare suke kwana a daki,danshi Rainon boss lion ne,saukar shiyayi daga jikinsa yace” lucky kakula kasa ka yarda ta huta kokadan,idan ta tsaya kuma just bite her,understand,jijiga jikinsa yayi alamun ya gane tare dayin haushi,ganin hakan ne yasa boss lion ficewa daga falon yabar sultana da lucky tare abunsu. Sultana kam tun da taga lucky ji duniyan gaba daya bayayi mata dadi ,numfashi ma dakyar take iya fitar wa dan ba karamin tsorata tayi ba jikinta kaman a tada jen sai rawa yakeyi ,cigaba dayi tayi dan wallahi tasan idan batayi bama zai sanine dan tasan gidanshi ne,yanada iko akan komai,idan batabi bama ita zata sha wiya,Lu koma dayake shima dan iskane ne sai ya wani zauna a waje daya yanata kallonta,duk dadai sa’an ta daya bai matso inda take ba ,shiyasa ta iya cigaba dayi har zuwa lokacin da boss lion zai ce ya’isa. ______________________________________________🥶 AFTER 40 MINUTES 🥹 Tun tana iyayi har abun ya gagara ,numfashita yana bara zanan daukewa,cinyanta yayi tsamin bala’i ,har ta fara dana sanin zuwa gidan,dan idai haka akeyi kullum to bada ita za’ayi ba,numfashintane ya dauke dipppp,jikinta ya saki,ya fadi akan carpet din,kafunta fadi wani abun al’ajabi sai ga lucky ya je ya tsaya a wajan ,cikin da bara irin na wannan Karen ya daga hanayensa sa sama wajan tareta dan karta fadi direct zataji ciwo,faduwa tayi a jikinsa kafun ya kwanta da jikinsa ya sauketa a hankali,dan irinsu lucky kawai ka gansu ka barsu dan ba karamin horo aka basu ba. Zagaye ya cigaba dayi a wajan ,suna haka saiga junaid ya shigo falon bakinsa dauke da sallama ,shiga yayi kwata kwata hankalinsa baikai kansu sultana ba yana wani waje ,har ya kusa isa jiki elevator,kaman da sama yaga lucky a gabansa ,Allah idan yace bai tsorata ba karya yake kawai dai ya mazge ne ,ganin lucky ne ya sashi Jan tsakin,ya hayayyako masa”kai wallahi lucky anyi dan iska ,wato ka dawo dole kazo mun oyoyo,Toh bari kaji kamun haukan anan kagani jikin ka ya gaya maka. Haushi lucky yayi masa yana kokarin nuna masa inda sultana take a kwance amma Ina bai gane ba,haya juya zai tafi,aikuwa yaja rigan sanyin dake jikin junaid ,yana haushi ya janyosa inda sultana take,ai kuwa sai idonsa ya kyallara masa inda sultana take a kwance kamar matacciya,ai baisan lokacin da yayi wufff ya isa inda ya gata ba,ganin yanda idanunta suka kumbura saboda kukan da tasha ,wani irin tausayin sultana ne ya kara kamashi,da baisan lokacin kuka ya kubce masa ba dan shikam ya gaji da ganin yanda yaya boss yake wahalar da baiwar Allah nan . Idan yasa bazai barta tayi jinya cikin kwanciyan hakaliba ai da ya nuna cewa shi bai yarda da zamanta anan inba. Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) Page 28 _______________________________________________🙏 Daukanta yayi ya ajiyeta akan kujera,dakansa yawuce cikin dan dauko ruwa,yana zuwa ya yayyafa mata”huuuuummmmm taja ajiyar zuciya ,tana fitar fa numfashi a hankali ahankali,sai kuma ya fara hawaye yana gagaro ta gefen idonta,ganin ta fara hawaye ne yasa junaid yayi sauri goge mata danshi tundazu ya gama nashi kukan. Tashi take kokarin yi danta zauna amma ina kafafunta ciwo suke mata ,ganin tanason mikewa wane yasa ya taimaka mata ta zauna dakyar,cikin muryan kuka tace “yaya junaid dan Allah inaso na koma gida ne dukda dai canma ba Jin dadin zama nakeyi ba,amma yafi zaman gidanan nesa ba kusa ba,dan indai na cigaba da zama a gidanan watarana saidai kuzo ku dauki gawana,,dan wallahi bazan BOYE maka ba yayaynka mun..gu..ne,ta fada a rarrabe saboda kukan dayaci karfinta ,bu buga bayanta yakeyi alaman rarrashi. Kafun yada go fuskansu suna fuskanta juna ,cikin rarrashi yace “meyasa kikeso ki tafi bayan bashi yace ki tafi ba,dan shifa yaya boss bazaka ce ke zaki yanke wa kanki hukunci ba,dan bazaki zauna masa a gida ba kuma kice lokaci daya zaki tafi ba,”kuma kodan ni bazaki zauna a gidan ba ,kinga fa kekadai ce kanwata dake dashi,dan Allah ki daina maganan zaki tafi kibar ni,kinji ko”eh gyada kai tayi dan ,itama tanason zama ,Toh amma boss lion yanada wiyan sha’ani. Yanzu ki fadamun,labarin ki,dan iso insan daga inda kika fito dahar zamancan dinma bai miki dadi ba”girgiza kai tayi tace”babu fah ya junaid ,ni banmasan na fada ba,”ai dole kice mun bakisan ma kifada ba”please sis sultee ki fadamun mun “Kodai baki yarda dani bane”a’a ya junaid na yarda dakai mana zan fada maka amma please karka fadawa kowa kaji “Shikkenan bazan fadawa kowa ba dagani sai ke sai kuma Allah. Gyada kai tayi ta fara bashi labarin yanda ta zauna Insha tana muzguna mata tare da yayanta ga babanta baya iyayin komai ,komai zasu mata bazai ce komai ba har rayuwansa da tayi a gidansu jabir ta bashi labari,harzuwa ana gobe aurenta da dare akazo aka sace,har gidan karuwai da aka kaita,zuwa lokacin da ta gudu ya bugeta,,share hawayen daya zubo mata tayi”tace yaya junaid kaji tarihin rayuwata ,karka gayawa kowa,ya zama sirri tsakanina dakai,gyada kai yayi idanunsa sunyi ja jin tarihin rayuwanta. Shikkenan dai yanzu tashi muje kiyi wanka,ki gasa kafanan naki da ruwan zafi kozaki samu yadauna miki ciwo”tashi tayi dakyar dan kafan harya fara yin tsami,riketa yayi ,shiko a jikinsa duk da ya kasance musulmi,amma rainon turawa,kwata kwata basusan wani abushi kunya ba,”dakyar take tafiya gar ya kaita daki ,ya fito ya barta dan tayi wanka ta shirya,yana fita daga daki tashiga toilet ta hada ruwa mai zafi tashiga ciki ,ta mammatsa kafafunta dan har su harsun yi tsami ,tanayi tana sharar kwalla,dan ba karamin zafi take ji ba. Bayan tagama gasa kafan tayi wanka shaf shaf ta fito ,tashiya cikin riga da wando,blue palazzo trouser with white t-shirt mai hade da Palmara shima kalan wandon,fuskan ta batayi kwalliya ba amma ba karamin kyau tayi ba ,ga kayan ya amshe ta badan kadan ba,gashi ta kara wani haske sosai kaman ka taba jini ya fito ,skin nata yana glowing,hutu danin dadi ,kaci mai kyau kasha mai kyau ,dole mutum ya canza,white veil ta daura akanta,tana shirin saka takalmi taji Ana knocking “yes come in”dan tasan baiwuce junaid bane,shigowa yayi . Ganinta yayi daga sama har kasa yace”sarauniyar kyau kinga yana kikayi kyau kuwa gaskiya ina kishi dake,duk kinzo kin fini kyau,sultana kam dariya takeyi jin yayabe ta ,taji dadi kuma”haba yaya junaid Nina isa nafi brother na kyau ne,”Nifa gaskiya bakiyi kama dayar Nigeria ba ,dan bakwa yanayi dayan can,dan ana ganin ki anga balarabiya “kai yaya junaid waya fada maka haka nikam yar can ce ,Toh naji yanzu dai ki sakko kasa yaya boss yana kiranki , karki bata lokaci fah, dan shi abun laifi baya masa kadan, yanzu sai punishment. Jin yaya boss yana kiranta tuni jikinta harya fara rawa tace “yaya junaid nifah nashirya muje kawai,Toh amma dai jikinki yadaina rawa,kijiko “Toh kafun ta saita kanta suka wuce dukda haka tafiyanta bai dawo daidai ba,a haka har suka karasa main falo,anan suka tarar da boss lion zaune a one seater yayi crossing na legs nashi,Ashman,uncle Ibrahim,uncle tareeq, suma suna zaune a falo ,ta tsorata da ganinsu duka a falo ,tasan ma cewa zaiyi tatafi tabar masa gida,dan taga alamun kwata kwata baisan wani abushi mutumci ba,dan sun raba hanya. Can dan nesa da boss lion ta zauna akan carpet,bakinta haryana rawa wajan cewa”good afternoon ta fada batare da ta kallesa ba,boss lion yi yayi kaman baijita ba sai daddana wayansa yakeyi,ta maida ko baiji bane yasa takara”cewa good afternoon,jin bai amsa bane yasa ta dago ,ai kuwa suka hada ido,wani banzan kallo ya jefa mata ,tare da dauke idonsa daga kanta,sultana kam ganin irin kallon daya jefah mata ne yasa ta dauke kanta kasa tare da gashe da su Ashman,uncle tareeq,da uncle Ibrahim ,sauran sun amsa cikin sakin fuska amma bai da uncle Ibrahim daya dauke kai kaman baisan tanayi ba. “Kibude kunuwanki kijini dakyau “boss lion ne yayi maganan amma zaka rantse bashi bane,danshi maganan sa a hakali yakeyi,”kinsan kimun laifi ko to wannan punishment din Dana baki bashi kadai bane”sauran punishment naki shine,breakfast 9:30am,launch 2:00pm,amma sai ranan danake gidan,dinner 10:00pm,coffee 11:30pm,muddin kika kiyi akan time,saidai ki koma kwana a dakin lucky,nagama magana kuma da dike cewa zaki koma inda kika fito Bismillah,every time the get is open. Zaro blue eyes nata tayi sai sheki yakeyi saboda ruwan daya taru a cikinsa,jin cewa zai maidata dakin lucky bakaramin daga mata hankali yayi ba,kuma tasan yanda yaya boss yake bashida mutumci zai aikata,Toh amma abunda ya bata mamakin shine yanda akayi yaji cewa zata bar gidan,yanzu kam ta fara kokonto dakyar idan yaya boss ba aljani bane,dama kyansa yayi yawa ,harya fita a suffan mutane,ga mugunta dama aljanu ansansu da shege mugunta,idan kuwa ba aljani bani ya hada dangi da mayu,maganan da yayi ne yadawo da ita daga tunanin da takeyi. “Kuma ni bana harka da some one illiterate,dole ki shiga school,kuma wallahi na sakaki a school kika kiyin karatu,I will deal the hell out of you,”I won’t take nonsense,did you hear me,gyada kai tayi jikinta duk yayi sanyi,cemata dayayi illiterate ya bata mata rai,amma cewa da yayi zai maida ta school ba karamin faranta mata rai yayi ba kuma saita nuna masa,saidai shene illiterate wallahi,sai wani dogon warning dayake mata. “Dan ma baki yi karatu ba to zaki biyani kudinane dan bazan dauki asara ba,but if you think am joking’try me and see,yana gama fadan haka ya fita daga falon dan akwai abunda zaiyi,dan bayason Africa time kwata kwata. Mutanen cikin falon kuwa ba wanda ya iya cewa uppan,sai dai sunyi farin cikin jin cewa zai maidata makaranta,dan abu mai kyau ne,kuma shi boss lion duk muguntansa yana kyauta sosai ,baya kyashin kashi konawa ne,akwai sanin ya kamata kam ba laifi”cewa dayayi idan batayi karatu ba zata biyashi kudinshi saida Ashman da uncle tareeq suka murmusa,junaid kam dariya ne yaso kub ce masa jin abunda yayan nasa ya fada,uncle Ibrahim kam taki yaja tareda cewa”yanzu idan ba asara ba mai zaisa mutum kaman boss lion yace zaika ta a makaranta,Allah yayi wadaran naka ya lalace,yafada tare da barın wajan cikin takaicin jin abunda boss lion yayi. Ashman ne ya matso wajanta,jiyayi ya kasa dauke idonsa a kanta dan ba karamin kyau sultana ta mishi ba,shifa tun ranan daya fara ganin ta sai da wani abu ya darsu a zuciyansa “sis,ina taya ki murnan zaki koma school,amma fa saikin maida hankali wajan yin karatu ,dan duk abunda kikaji yace Toh saiyayi muddin bakiyi karatu ba,nasan bazai dauki lokaci ba zaki fara tafiya school,byee,shima wuce wa yayi dakinsa yana gama fadan hakan,ya saura daga junaid sai uncle tareeq,uncle tareeq ne ya matso zuwa inda take yasha kanta yana murmushi yace”Allah yayi miki Allah yata,kuma ya baki ikon yin karatun,”mayar mishi da murmushi yayi tace Ameen nagode uncle,gyada kansa yayi tare da fita daga falon ,ya nufi waje,ya rage daga ita sai junaid. Rungumeta junaid yayi yana dariyan farin ciki yace”one and only sister am so so happy for you,dama inataso na miki magana akan makaranta sai wani abu ya dauke mun hankali na,amma naji dadi tunda yaya boss ya tsara hakan,”yaya junaid bazan iya misalta maka farin cikin da nake ciki ba, nagode muku yaya junaid Allah yasaka muku da alkhairi,shhhhiii ya İsa haka bamasan godiya komai mun miki ne saboda Allah,kinji ,kinga yau tanan farinciki ne awajan zu muje,yaja hanunta suka wuce sama. Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) Page 📃 29 ____________________________________________❤️‍🩹 NIGERIA 🇳🇬 Gombe😇 Tunda sultana ta fita daga gida kowa ya wuce dakinsa danya kwanta,basu damunda sultana ta shigo gida ba ko akasin haka,saboda San zuciya irin nasu,irin idan taga dama ma ta kwana a wajan,duk dai sunsan zata dawo,haka suka kwanta bacci ba wanda ya sake suna cewa sultana fa bata shigo cikin gida ba,ba addu’a ba komai haka suka kwanta,saboda jahilci dayayi musu katutu. Asuba ta gari ****** Sai wajan karfe takwass suka tashi daga baccin asaran daya dauke su ,ko sallan asuba basuyi ba,kuma a hakan akwai daurin aure a gidan,tashi sukayi sunata hada hadan biki abunsu,kwata kwata basu lura da babu sultana a gidan ba ,dama ance ido bashine gani ba hakali ne,wata makociyar su maisuna,baraka ce take tambayan ina amaryan take ne ,bamu ganta ba,innaah tace”ohh ki bar shigiyar yarinyar nan yanazu haka tana can ta dukun kune waje daya,ita a dole batasan auren”amma badda abinki Ladidi(asalin sunan inaah) taya zaku bawa yarinya mai jini a jika yaro nan garbati,kowa fa yasan,yaron nan dan daba ne,”kuma naji a gari anacewa dakyar idan basida AIDS, “kijiki ko sai ana magana hankali ki dauko na rashinsa. Ina ruwana aini haka nake so,nafiso naga ya wulakanta a rayuwa ,wallahi koganin fuskan yarinyar nan banason yi,ni inbanda kaddara ma maizai hadani da jini aljanu “saurin katseta baraka tayi “haba haba ladidi wannan fah ba dai dai bane,yanda kayiwa yayan wasu haka za’ayi wa naka,yanzu ace za’a aurawa habiba,deeje,ko zulaihat ai bazaki yarda ba soboda kinsan cutansu za’ayi…..”A’a kam badai yara naba bakinki ya sari guntun kashi ,kinga idan abunda kikazo yi kenan ki tashi ki tafi umma ta gaida aisha ai dama bamu gaiyace ki ba,gulma irin naku ,ya kawo ku da shishigi “Allah yace ki sowa dan uwanka abunda kaso wa kanka,”kuma ina dai ni kika yi wa gori,Toh bari kiji kiyi da yar halak,idai na fita daga gidan nan bazan sake zuwa ba . “Yooo dama waya rike kafanki,ga hanya ,kuma dakike cewa nayi da yar halak,ce miki akayi,nidin suntoni akayi daga sama,kuma aure ne dai yau sai an daura ko kuna so ko bakwaso,wannan ku ya dama,”barka ba abunda tace mata ta tashi tanufi hanyan fita kenan taji wani hayaniya na tashi a gidan,gulma na cinta batasan lokacin data koma dan kar ayi ba ita. Zulaihat ce ta fito da gudu tana cewa”inaah wallahi sultana bata dakin mu ,bana ma tunanin a gidanan ta kwana ,na mafi tunanin guduwa tayi”ke banason zancen banza taya zaki ce baki ganta ba bayan,ba inda yarinyar nan take zuwa,”tana haki tace wallahi innaah da gaske nake bata dakin nan,”matsamun na shiga nagani,shasha shar yarinya,sai son jawa mutane bala’i ,tafada hade da shigewa cikin dakin ,tashin senses! Ba taga sultana ba,ba inda bata duba ba,har kasan katifa,su bayan akwatinta,bayan kofa,duk ta duba ,dakinda kallo daya zakayi mishi zaka gane idan akwai mutum ko babu. A haukace ta fito daga daki ta kwalla wa sultana kira,sultana sultana sultana amma,shiru mutane duk sunyi cirko cirko ,dan gulma,deeje ce tayi karfin halin cewa”innah Toh a duba mana ko tana bandaki ne”aikuwa yar albarka,amma kuwa idan na kamata acan jikinta saiya gaya mata,bandaki suka shiga ba excuse ko ,a’a kawai shiga sukayi kaman sun samu dakin uwarsu ,sai dai me,suna shiga suka samu wayam ba kowa,dakyar aka da ina aka dawo da ita tsakar gidan ,sai zage zage take yi”shegiyar yarinyar nan ni zata wulakanta ta gudu,sai ga innah ya fara matsar kwalla saboda takaici ita kaidai tasan irin kudin garbati dataci duk dadai shema na haramun ne kuma ba barinta zaiyi ba. Yanzu haka tasan suna masallaci wajan ankusa daura aure bai wuce saura minti biyar ba. Bayan minti goma sai ga garbati da tawagansa sun shigo cikin gidan yasha wata shaddansa sabo ,kana ganinsa kaga ransa a bace yake saboda rainin hankalin da innah ta mishi ba kadan bane,Abba biye dasu a bayan shi,bazaka gane ransa a bace bane ko kuma akasin hakan,tun kafun su garbati suyi magana Abba ya miko mata ,goro da su chewing gum,yace”yau dai nasan burinki ya cika kuma nawama ya cika a matsayi na na uba,bayarda auren yata Habiba wa garbati,yanzu haka sunzama miji da mata ,sai ki musu addu’an Allah ya sanya alkhairi. Kururuwa innah ta fara a wajan,sai ga habiba ma ta Zube a kasa sumammiya “wallahi baka isaba,aure dai. Bazai taba yuwuwa ba,hauka kakeyi ne malam da zaka bawa dan shaye shaye yarka,ko an daura saiya sake mun yata,yata bazata taba zama da wanan mutumin ba,gwanda ma kaji kasani. Sai kuma tace “wayyou Allah na ,nashiga uku na lalace, abban habiba ka cucemu cuta mafi muni”ba wani cutankin danayi kefah da kanki kika zabawa sultana kuma gani nayi kema uwa ce,bazakiji komai ba idan aka bada yarki,dan haka ki shirya na baki nanda hour daya za’a wuce da ita dakin mijjinta,malam wallahi bazai……….”ke innah kike kowa wallahi yanada kika damfare ni kika ce zaki auramun sultana ,kuma kika boyeta to kisani,kisa wannan a bayan kunnenki,sai na fanshe duk kudina dakika ci a jikin yarki,yana gama fada haka ,shida tawagar sa suka fita a gidan. Harya fita kuma sai ya dawo yace”ki tabatar ankai ta akan lokaci idan ba haka ba kuma kinsan saura,ya fice daga gidan.”wayyou innah kin cuceni, tana kuka harda shide wa ,”wallahi ni ban shiyayi aure ba yanzu,kuma kona shirya ai bai kamata,a hadani da garbati ba dan giyane fa mai biye biye mata. Guda ,barka tayi tace,oh yayanso ,shinan dai abunda nake fada miki kika nayar dani yar iska,yanzu abunda ya rage kawai tunda tayi wanka a bata kayan da aka ajiye wa sultana ya saka ,Toh habiba asha amarci lafiya,nabarku lafiya,yau nayi farin cikin da na dade banyi ba wallahi,tana magana tana kwasan dariya abunta ko a jikinta,ta wuce gidan ta. Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) Page 📃 30 ___________________________________________🥰 Haka innah taka habiba suka shiga daki ,harda rufe kofan,saboda kar wani dan gulman yajisu,innah ya dubi habiba tace,karki damu bibalo,kiyi hakuri akai ki ,nikuma zansan yanda zanyi daga baya”cikin kallon kin raina mun wayo tace”innah har ce mun kike yi inyi hakuri akai ni wannan gidan. Hmmm, ai wallahi bazata sabuba,gwanda ma tun wuri ki fada musu ya sakeni Dan bazan yi wanan zaman auren ba,”dadina dake bakya gane wa,kibari akaikin niku zan wuce gurun malam zarfuru,maje na amso miki ɓaganin da sai abunda kike so zaiyi wanda ba kyaso bazai yi ba ,zaki mayar dashi tafin hanun ki ,ki juyashi yanda ranki yake so. Cikin gamsuwa da abunda innah ta fada tace”yauwa innah ta shiyasa nake sanki,kuma hakan yayi daidai,wallahi,sai innah ta ,ta fada cikin jindadi ,innah tace “yar banza dazu dana ce miki ki yarda har wani kallon bakida hankali kika mun,yi hakuri mana innah kinsa a lokacin ba a hayyaci na nake ba. Shikkenan dai kiyi sauri ki shirya ,dan danasan kinyi wanka,kinga lokacin da malam ya bamu yana tafiya,maza maza,bari nakawo miki kayanda yar yarinyar nan ta gudu,ta fada hade da fice wa faga dakin . Cikin kankanin lokaci hafsat ta shirya ,kuma gaskiya tayi kyau,dan itama badai body ba,ga breast dinnan a kwaishi saidai har sun dan kwanta ,saboda biye biyen mata,hips ma dai a kwaishi ba laifi,innah ce taja gyalen ta rufe mata fuska dan yan dauka amarya sunzo ,fito da habiba akayi daga daki ,sai a lokacin su deeje,da zulaihat suka ganta,tare suka rungume ta ,tare da fashe wa da kuka ,yanda suke kukane yasa habiba kuka ,daga baya kuma ta rarashe su ta nena musu ba komai. Dakyar aka bambare habiba zaga jikinsu ,aka fitar da ita waje,mota daya ne a wajen shima golf da duk ta tsufa dakyar take tafiya,bayanda zasuyi haka suka saka habiba a cikin motan suka tafi, kafun su isa kayan cikin ta duk sai da suka jijiga ,ga motan baya gudu kokadan,haka suka isah gidan garbati dake cikin anguwansu sultana,dan ba shida nisa sosai dasu. Fito da ita akayi daga motan ,gidan kana gani kasan na haya ne ,shiga sukayi tare da wasu yan uwanta mata da suka kawo ta ,gidane mai kofa 8 daki dayane da kitchen dan karami sosai ,haka ko wanne yake,ga kazatan kwata gidan dai ba kyan gani kokadan , cikin gudan daya daga cikin kofan suka wuce da habiba har cikin dakin ,bakomai sai wani taburma da wani yaloluwan katifa dayaji jiki ba kadan ba. Matan da suka kawota ma tafiya sukayi dan sunga bazasu iya zama a gidan ba ga hayaniyan yara da guje guje,haka suka tagi sukabar habiba ita kadai a dakin ,sai harar hawaye takeyi,ganin inda rayuwa ta kawota ko a mafarki bata taba tunanin haka ba,haka ta zauna ita kadai a daki bata fita ko ina ba,har dare yayi bataga alamun mutum ba,dan jiran innah take yi takawo mata maganin tasan yanda zata yi kafun garbati ya shigo,haka har akayi isha ba taga giɗmawan kowa ba ga yunwan dake nanukan ta, a haka har bacci ya dauke ta batare da tasan lokacin daya dauke tanba. Cikin baci taji ana shafa mata albarkatun kirjinta ,a firgice ta tashi ,garbati tagani a kanta daga shi sai gajeren wando ,bakinsa duk warin taba,baya baya ta fara ja “haba wa baby ,yau fa sai dai kiyi hakuri dan ba abunda zai hana na kusan ceki,wanda kin bada hadin kai kawai muji dadin mun dan nasan kema ai yar hanu ce,yana fada haka ya hade bakinsu ,habiba ta rasa yanda zatayi bakinsa wari baya brush ga warin taba ,haka ya danne ta ya cire mata kayan jikinta duka,baiyi wata wata ba ya shige ta da karfin gaske. har asuba yana abu daya ,habiba ba karamin galabaita tayi ba a hanunsa dakyar take iya daga hanunta saboda bakara min wahala ya bata ba ,a haka bacci ya dauketa bata tashi ba sai karfe takwas ,jikinta duk yayi tsami , garbati baya nan ya tafi harkan gabansa,tafi tayi tafita wajan gidan ta samu wani yaro ta tambaye sa inane bandaki ya nuna mata ta koma daki ta bude Gana most go din kayanta ta dauki soso da sabulu sai bucket din da ta samu a kitchen ,tajeta baki rijiya ta iba ruwa tashiga bandaki tayi wanka dakyar dan bandakin kazanta yayi mishi yawa ,tana kowa daki ta tarar da zulaihat ta kawo mata abinci. Taji dadi ganin kanwar tata sosai shiryawa tayi cikin kayanta ,ta zauna tacı abinci dan ba karamin yunwa take ji ba,bayan tagama cin abincin suka ha hira abunsu,sai yamma kafun zulaihat ta tafi. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya ,habiba kullum sai garbati ya kuce gajiyansa a kanta,kar ya samu jaka tun tana kuka har ta saba, ba kullum yake kawo mata kayan abinci ba sai ya ga dama ,haka take manage na abincin ,akwai sauran kudin da samarinta suka bata data ke tarawa ,dashi take samu ta siya garin kwaki ta ajiye,,har yau bata sake ji duriyan innah ba ,hayi jiran harta gaji,wani lokacin zulaihat tana zuwa tayata hira ,gashi bata shiri da matan gidan hayan,abun ya taru yayi mata yawa sai uban zaman da tayi. Garbati wata Rana idan ya dawo gida a buge ,duka ya ke mata na fitan hankali,har faffasa mata jiki ya keyi,ko a jikinsa ,tuni habiba ta fara nadama abubuwan da tayi ,ga bala’i tsoron garbati take yi kaman mala’ikan mutuwan ta. Dan bashida kirki ko kadan ,saidai ta zauna tayi kuka ,har kuka ya zama abokin hiranta ,duk tabi ta lalace kaman ba habiba ba,Toh amma ya zatayi haka zata cigaba da hakuri dan garbati fah sai addu’a. Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) Page 📃 31 ________________________________________________🥹 USA 🇺🇸 Wishing tone Yau Saturday takama 2 weeks da zuwanta gidan boss lion,kwance take akan gado ,jikin ta sanye da abaya peach color da design na rose a jiki kayan yayi kyau,kuma ta karawa kayan kyau da ta saka,sai kamshin perfumes takeyi masu masifar dadi,ga gashita yasha gyara duk da dakyar ta samu tayi parking nashi saboda yawan gashi ga tsayi ga cika ga laushin masifa,dan gashin nata har wajan bom bom nata.fuskanta fayau ba abunda ta shafa a fuskan Banda lotion,damuwa ne yasa ta kasa shafa komai a fuskanta, amma duk da hakan ba karamin kyau tayi ba,ga wani earring da neck pendant data saka sukuma red ,color rose din jikin rigan,sai kyalli take yi tana haskawa. Fuskanta dauke da damuwa,dan tasan yau zata fara yin punishment din da boss lion ya saka ta,batasan ma yazata yi ba,karta je yin wannan punishment din ta sake wani laifin,dan taga alamun abun laifi baya mishi kadan,daga kanta tayi ta duba metal wall clock dake dakin da akayi design na pink rose a jikin wajan ba karamin kyau yayi ba,8:30 tagani saura 1hour time ya cika ,gyara zamanta tayi tare da jingina jikinta da akan gadon ,lumshe idonta tayi. Take kwakwal wanta da idanunta suka hasko mata kyakyawan fuskan boss lion duk da a hade yake yanda tasa ba ganinsa,idonta a lumshe sai faman saki murmushi take yi ita kadai,bata masan tanayi ba,ta bata kusan 1 hour a haka sai Tunani takeyi tana murmushi kaman wata sabon kamun hauka, a firgice ta bude idonta ,bai sauka a ko’ina ba sai wall clock,ganin 9:23am tashin hankali saura 7 minutes time ya cika ,batasan lokacin data zari veil nata dake kan gado ba ta fita a dakin da sauri sauri gudu gudu. A falo suka hadu da junaid ,dan tashinsa kenan daga cin abinci zaije wajan sultana yaji takai ma boss lion ne ko akasin haka,yana ganinta yasauke ajiyan zuciya yace”sis sultee wajanki dama nakeso nazo sai kuma gaki,katse shi tayi tare da cewa” yaya junaid dan ina yaya lion yake ne ,wallahi bansani ashe time ya kure,dama abunda nakeso na tambaye ki kenan ,kiyi sauri muje kitchen ki karba kafun kiyi wani laifin,dan ba ruwansa bata miki rai zayyi “Toh Toh ya junaid muje da sauri kafun time ya cika. Gaba junaid yayi sultana tana binsa a baya har suka İsa babban kitchen daya amsa sunansa kitchen ,suna zuwa dama kukun yariga da yagama hada komai da komai a babban tray mai bala’in kyau da tsada,junaid ne ya dauka suka fito dan yasan idai ya bar mata akan ta dauka sai sunkara bata lokaci,sauri sukayi suka isa wajan elevator ,within some seconds suka fito suka nufi bangaren boss lion . Sultana dai kam yar kallo ta zama dan bata taba zuwa nan area ba sai yau,wajan karamin tafiya daita yayi ba ,hmmm sultana kam sai tazama yar kauye😂,jijiga kai kawai takeyi kamar kadagare ,sai da suka tsya abaki kofan da zai sadaka da ainihin inda boss lion yake,mika mata tray yayi tare da cewa “ki tsaya ki ga yanda password din yake dan bakowani lokaci bane nake nan ,tsayawa tayi tana kallon yanda ya saka password din kuma ta gane ,dan fa sultana akwai kaifin basira bana wasa ba. Kallon junaid tayi tare da cewa”yaya junaid to mushiga tare mana dan wallahi tsoro nake ji nayi masa wani laifin ya dukeni, sake baki junaid yayi yana kallonta yace”yaya boss dinne zai dukeki to ke idan dukan zaiyi ma mezai samu ajikinki,ko kuma cemiki akayi yana duka,koya taba dukanki ne? Ya fada yana kallonta ,girgiza kai tayi idonta harya fara tara ruwa dan taga alamun abun da ta fada ya fatawa junaid rai . Yaya junaid kayi hakuri ba haka nake nufi bafa”shikkenan ya wuce amma kidaina yanke wa mutum hukunci da baki tabbatar yayi ba kiji “Toh ,Nina tafi kiyi sauri kikai kafun kiyi wani laifin,gyada masa kai tayi ,shikuma yabar wajan ,tunani takeyi tashigane kokuma dai ta fasa,shiga tayi zuciyanta sai bugawa yakeyi da sauri da sauri yakeyi ,falon tashiga harta shagala da kallon haduwan wajan sai kuma ta Tuna abunda ya kawota ,rasa ina zata wuce tayi dan kofofin suna daya wa ,wuce wa tayi wani kofa ta shiga shima wani falon ne har yafi wancan haduwa shima wucewa tayi dan taga wani kofa tana tunanin anan zata ganshi. Murda handled din tayi zuciyanta sai tsananta bugawa yake yi,kofan ne taji ya budu alamun ba’a rufe yake ba ,a hankali kaman barauniya ta shiga ciki ,wani irin sanyi ne da kamshi ne ya bugi hancinta,batasan lokacinta data lumshe idonta ba,kaman a sikare ta sai ta dawo hayyacinta dakin ta ke karewa kallo ,tana jinjina irin dukiyan da aka kashe ,aljanan duniya,dubawa ta farayi kaman muna fuka ko zataga boss lion sai kuma bata ganshi ba ,Ajiyar zuciya ta yi ganin baya cikin dakin”gwanda na ajiye na gudu kafun ya dawo ya tarar dani. Tafiya tadan yi mai nisa dan bakaramin girmane da bed room dinba ,wajan resting chair ta nufa ta ajiye abincin ,tana ajiye ta juya da nufin guduwa daga dakin kwatsam taga mutum ya fito daga dressing room,jikinsa sanye da farin wando da farin riga masu kafansa sanye da silifas na zaman daki shima white color hanunsa daure da farin agogon diamond me kyau da tsada,gashin kansa ba karamin gyara yasha ba ,ya kuma take gashin nasa baka iya ganin fuskansa sosai ,ga wani kamshi daya keyi,kaman yayi barin turare. Tsaya wa yayi ya kalle ta da mamaki ,amma sam fuskansa bai nuna hakan ba,kaman yanda yake kulum fuskanan a tamke kaman anyi gobara ,wuce yayi ya zauna a gefen gadon tare da janyo system nashi ,sultana dake tsaye tsoro duk ya gama cinta ko gaishesa ta kasayi,ganin hankalinsa yanakan system ne yasa tayi sanda zata futa,harta kama handle din ,kaman daga sama taji muryan muryasa “ if you dare go out,Hmmm abunda ya fada kenan, dan yan miskilancin suna kusa. Sultana kaman zuciyan ta yanda yake bugawa zakayi tunanin wani ciwon ne da ita,tana tsaye a wajan bata motsa ba ,ita bata dawo ba kuma ita bata tafi ba, tsayawa ma tayi tana karewa daki kallo, azuciyanta tace”daki sai kace aljanna (ni nace hmmmm sultana ai aljanna daban yake)”maida idonta tayi kansa bayansa kawai take gani, tana mamakin mutumin ,”mutum kaman basa mude ga tsayi ga ingarman ji,idan ya kama ka kashiga taran ka dan uku yayi kadan itadai Fatan ta Allah ya rabasu lafiya. (Sultana ina miki fata rabuwa dashi lafiya) Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️ *_💋SIRRIN DAKE BOYE_*❤️ ( The hidden secret 🌹) Page 📃 32 _______________________________________________ ✍️ System yake operating hankalinsa kwance,sultana a tsaye ya bawa banza ajiyanta,a kalla takai 30minutes a tsaye ,ko sau daya bai dago ya kalla inda take ba,sultana kam ba karamin gaji ya tayi ba ,a zuciyanta tana cewa”wannan mai fuskan shanun yazo ya wani tsayar dani,fisabilillahi sai kace wata soja ko police,ni kafafuna ma ciwo sukeyi wallahi. Mike wa yayi batare daya kalli inda take ba ya wuce wajan data ajiye abinci ya zauna,ba Uhmmm ba u’uhmm,ganin ya zauna a wajan abincin ne yasa sultana cikin sanda ta matso inda ya ke,ganin tayi sai faman lumshe ido yakeyi kaman maijin bacci,hakan da yakeyi kuwa ba karamin tafiya da imaninta yayi ba,dan boss lion fa karshe ne,sai kayi tunanin ma da gayya yake yi irin wannan abubuwan amma it’s by nature. “Good morning “muryanta na rawa ta gaishe shi dan saidata Aro jarumta ,banza yayi da ita kuma sarai yaji ,amsa wa ne kawai bazai yi ba,”good morning “ta sake gaishe shi a tunaninta ko baiji bane duk da tasani bai taba amsa gaisuwanta ba,nan ma bai amsa ba ,ganin ba amsa bane ta gane da yaji amsa wane bazai yi ba. Tsugunnawa tayi a gefen food flasks masu bala’in kyau ,white and golden, cikin nutsuwa tayi serving nashi abincin dan junaid ya fada mata idan takai sai ta tsaya ta yi serving nashi,amma saboda tsoro dazu tayi niyan guduwa ,Tana gama serving nashi ta tura mishi abincin irin nasu nachan, ta tashi tabar wajan ta koma Chan wajan kofa ta tsaya,batare da wani damuwa ba yafara cikin abinci a hankali ,idan kaga yanada yakecin abincin zaka dauka yanga yakeyi ko jiji dakai ,amma haka Allah ya halice sa bai iya cin abinci da sauri sauri ba ,cikin nutsuwa yakeyin komai. Sultana kam tana makale a jikin kofa,duk a tsorace take ,dalilin dayasa ta tsaya a jikin kofan shine,idan boss lion yayi niyan yi mata mugunta zata arce ne(idan Banda abun sultana,mutumin dakike zaune a gidansa ne zaki ce zaki gudu ) tana tsaye harya gama cin abincin ,bayan yagama bai bata daman kwashe kwanunkan ba gashi bazai yuwu ta ,tafi tabar masa ba a dakin,sai daya dauki kusan awa daya yana zaune yana latse latsen wayan dashi wallahi harga Allah ya manta ma dawata sultana a dakin . Sultana kam kafafunta sai rawa sukeyi saboda tsayuwa tundatazo dakinan a tsaye take kusan awa biyu ake nema,sai sharar kwalla takeyi,Tana jinjina mugunta irin na mutumin nan,kwata kwata lamarinsa ba sauki,mugunta kawai ya saka a gaba,banda komai,mai fuskan shanu kawai ta fada tana zumburo dan karamin bakinta gaba,(sultana zata kasheni da dariya😂🤣wai mai fuskan shanu saboda kullum fuskansa a hade no nonsense). Tashin da yayi ne ,idonsa ya sauka akan kwanukan abincin dake gabansa,take ransa ya baci,dashi ya tsani kazanta,abunda yakeyi a wayanne ya dauke hankalinsa bai Lura da cewa ba’a dauke kwanukan ba,juyawa yayi ta inda sultana take,kallon kasan ido ya mata ,zaka rantse ba ita yake kallo ba,wani wajan yake kallo. Baiwar Allah sultana ita kam sai faman mammatsa kafanta takeyi,dama na up and down bai warke duka ba gashi tsayuwan datayi ya fama mata wannan ciwon,shiyasa take mammatsa wa tanayi tana kuka mara sauti dan kar ya jita ,yace zai bata wani punishment din. Ganinta da yayi sai wani mammatsa kafa takeyi ne yasa shi tabe dan mitsitsin reddish lips nasa masu matukar daukan hankali ,ko a jikinsa wa wuce toilet,batare daya kalli inda take ba,sultana kam ganin ya wuce toilet ne yasa tayi sauri ta kwashe kwanukan ta fita daga daki,dan jikinta har rawa yakeyi Allah Allah takeyi ta fita kafun ya fito daga daki. *** Tana fita daga part nashi ta sauke ajiyan zuciya har sau uku dan ba karamin dauriya da jarumta tayi ba kafun ta iya fuskantan wannan mutumin,elevator ta hau ta sauka kasa,kitchen direct ta wuce anan taga sojoji chiefs sunata aiki dan ,gidan komai sojoji ne sukeyi,ba wanda ya tsaya kallon inda take ,kowa aikin gabansa yakeyi,suma dai kaman ogan nasu fuskansu a hade,dan suma koyi sukeyi dashi. Dakinta ta wuce ,tana zuwa ta fada kan gado tare da rugume pillow a jikinta,dan har yanzu bawai ta gama dawowa seti bane,tunanin abubuwan da suka faru takeyi,”murmushi mai kayatar wa tayi dimple nata suka lotsa,masha Allah zallan madarar kyau ,bakaramin kyau tayi ba datayı dariya ba, “Lallai yau na sake tabbatar wa da cewa mutumin nan miskili ne yau asalin yan miskilancin suna kusa,dan tunda taje sau daya yayi magana,shima kaman wanda a ka sakashi dole. Batasan meyasa ba,tanajin farinciki idan tana ganinsa koda kuwa muguntan zayyi mata . Ahaka har bacci mai dadi ya dauke ta tare da mafarkai masu ban sha’awa da kyatarwa,ita kadai takan ne ta gani a cikin mafarkin nata. ❤️‍🩹~<>~<>~<>~<>~<>~<>~<>~<>~<>~<>~<>~<>~🌹 2:33pm Sai lokacin sultana ta tashi daga bacci daya dauke ta ,tana tashi abunda ta fara dubawa shine time, tana ganin time dinan tuni Tasha jinin jikinta ,dan 2:30pm yace zata tana kawo masa abinci,cikin sauri ta sauko daga kan gadon ta wuce toilet ta wanke fuskanta kafun ta fito ta nufi hangar waje ,tana fita sukayi kicibus da junaid da shima dakinta zai shigo,hanunsa rike da wani laida mai girma. Wuce shi sultana tayi,hankali ta duk baya jikinta bata ma Lura da junaid data wuce ba,saurin rike hanunta junaid yayi tare da cewa”sis sultee ina zakije har kika wuce ni baki gani ba,naga alamun ma ba’a cikin hayyacinki kike ba”sorry ya junaid wallahi bansan ma kana wajan ba,hankali na gaba daya yana kan abincin yaya lion,bacci ne ya dauke ni batare Dana shirya ba kuma sai na makara,yanzu sai ya sake bani punishment,dan nasan bazai barni ba na bankai masa abinci da wuri ba. Shikkenan nan ki kwantar da hankalinki dan yaya boss bayama gida amma fa ki kula nan gaba,karki na yin latti wajan kai masa abinci kinji ko”Toh tace sai yanzu taji dama dama,”yaya junaid mu shiga daga ciki,nazo na tsayar dakai a waje”shiga sukayi cikin dakin,junaid ya zauna akan two seater dake daki ita kuma sultana a one seater ta zauna ,laidan daya shigo dashi ya mika mata yace”sis ga shi ki bude ki gani. “Toh”tace tare da bude laidan ,da masu uniform masu bala’in kyau taci karo dashi blue-black colour ,da white shirt mai hade da necktie shima blue-black colour ,sai skirt maroon color sai mini hijab white color , sneakers black color ga school bag guda 4 a ciki,black,pink,white,nevy blue,uniform kala 5 ,sneakers kala biyar(5) kayan bakaramin kyau ne dasuba ga shegen tsada kaman me,sultana tana ganin taya,saboda farin ciki ,she can’t even control tears. Ya junaid gabasan dame zan saka muku ba saidai nayi muku addu’a Allah yasa ku a gidan aljannatul firdaus,kullum cikin sakani farin ciki kukeyi Allah ya bani ikon sanya ku cikin farin ciki wata rana. Ameen ya Allah,mun gode da addu’a ,mu dan Allah muka miki,kuma ki share hawayenki ba kuka ya kamata kiyi ba farin ciki ya kamata kiyi,banason ganin damuwa a wannan kyakyawan fuskan nan,mur mushi ne da kunya suka Kama sultana ,ta sukuyar da kanata kasa tana murmushi “Yauwa koke fa har kinfi kyau,inda kina kuka bakya kyau. Mikewa yayi tare da kallo sultana yace”sis nikam na tafi akwai abunda zanyi sai ajima”bye bye ta masa,shikuma ya fita daga dakin. Yana fita sultana ta daga hanusa tana godiya ga Allah ya canja mata rayuwa,daga na bakin ciki zuwa farin ciki) Ranan wuni sultana tayi a daki cikin farin ciki itama zata fara zuwa makaranta,sultana tana da kaifin kwakwalwa da saurin daukan abu da wuri,wayo,. Ajiyar zuciya taji ,tare da tunanin yanzu dadarenan ko ya zasu kare da boss lion ,wata kila bazai barta ba sai 2:00am zai ce mata ta tafi ,ita batasan ma ya zatayi da wannan mutumin ba. Alhamdulillah,Alhamdulillah,Alhamdulillah Anan na kawo karshe book 1 &book 2 paid ne Wannan littafin na kudi ne 300 ne kacal ba yawa ga mai bukata ga wannan account number 7068845514 OPAY Fatima mala umar,zaki iya tura shaidan biya ta wannan number 08161857656 Nagode 🙏 2024/2025🔥 Story and written by AMID ✍️