*CI GABAN BINTA YAR JAGALIYA* Jifan gafiyar ɓedu *Ba tsuntsu ba tsarki* By Oum Yasmeen Book two Ban hanaki karanta littafi na ba amma kinsan Allah baya yafe hakkin wani a kan wani typing a kwai huya ki daure ki mallaki naki ba kuɗi mai yawa 300 kacal Ki yiwa Allah da Manzonsa ƙarki karantan littafina in kinsa baki siya ba sai kujera sai an gama littafi ku dinga ƙaramar murya a temaka a baku Dan Allah duk wacce ta siya ta ruƙe amana ƙarta fitarmin da book ɗina Tsohonwan shugaban ƙasa Alhaji mu'azzam kura ya ɗaga waya yace "Zaka iya shigowa , Ya katsai wayar ya ajjiye ba jimawa sai ga muzabfar da Alhaji mansur kahun mu'azzam sunyi sallama hannu suka miƙawa kahu labahani suka gaisa samin gun sukai suka zauna Kahu labahani yace "To kafin a daura aure ina da magana, Alhaji mu'azzam kura yace Muna jinka Ina da yayana shima kahun binta ne uwar mu ɗaya uban mu ɗaya shi nake bi sannan sai mahaifiyar binta bilkisu Allah yayi mata rahama ko za'a je can unguwar hayar tudu a daura ko ba komai mutane sun sani sannan zan gyara kuskuran da nayi abaya na tora bilkisu aikatau Makka ta dalilin haka ya ji haushi mukai faɗa yau shekara goma sha tara kenan shekara ɗaya da rabi ta dawomin da ciki tace aure tayi yar ta ba shegiya bace sosai ran malam Umar ya ɓaci ya bar gidan da nake ya tafi unguwar hayar tudu ya zauna Sosai muzabfar ya ga hankalin kahu labahani yace A gaskiya ƙimar ka ta daɗo a gun mu Insha Allah za muje da Kai ayi komai Alhaji mansur yace "Ƙar ka damu mun aminci da manshi aure shedu yake so kar axu ayi ɓatatciya ko baffa , A jiyar zuciya yayi yace Mun amince yanzu zansa a Kai Ka gida kafin gobe muje farin ciki ne ya mamaye zuciyarsa domin yana ganin zai gyara a laƙarshi da dan uwansa sannan koda Binta ta ɓallo auranta ba shi kade zata gallaba ba har da malam ai mutuwar yawa kaka ce yace "Bakomai nagode Allah ya shege mana gaba, Ameen suka ce Wannan kenan Rufaida gobe zaki rakani inda ake siyan bizar Saudiya domin ina so in nemo mahaifina Murmushin manufa tayi tace "Ƙar ki damu a kwai dan uwan mamana yanayi zan raka ki wajansa ayi komai a xuciyarta kuwa cewa tayi hmmmm da alama ta shin hankali kika iya baki da wayo na sami damar ƙarɓe sauran kuɗin in tafi Lagos can in baza duniya ta, "Bara in koma gidan wai yau sati nawa da siyan gidan nan ne ?, Gaban rufaida ya faɗi domin hayar wata ɗaya ta kama komai ya kusan fashewa ya kamata ta fara haɗa kayan ta tayi gaba tace "Wata ɗaya ba kwana ukku , Okay na fa daɗe a ɓoye wallahi yau jina nake saka yau sai gobe ko Allah ya kai mu Ameen tace ta shiga cikin gidan ta shiga bedroom ɗinta tayi ta canza kaya zuwa wani material mara nauyi ash colour sai yarfin flowers black colour sosai tayi kyau zama tayi ta fara danne danne a waya kiran sallar magarib a kai tana ji ta tashi tayi domin duk abin ta tana kiyaye lokacin sallah ko tana club sai tayi ta toilet ɗin dake manne a bedroom ɗin ta shiga ta dauro alwala tana fitowa ta tarar da kiran rufaida share kiran tayi sai ta idar da Sallah zata amsa Wannan kenan Sosai acikin satin nan ran Hajiya Turai yake a ɓace da ba dan Alhaji ya hanata ɗaukan mataki ba da tuni tasa a kama Binta ji tayi kaf duniya ba wanda ta tsana sama da ita bata son ganin ta abin da ya sassauta mata fushinta nasarar da ɗanta ya samu gir giza ƙafa take tana zaune jiran dawowar ɗan nata take taji daga bakin sa Alhajin kura ya faɗa mata wata magana wacce ba zata taɓa lamintar ta ba ɗan ta ɗan sunnan ya aure shegiya yar tiktok wacce ta fito idan duniya ta ce mai mazinaci har tofa masa yahu tayi Wayar ta ta ɗauka ta fara kiran sa har ta ƙari ringing ɗinta be daga ba tayi tsaki yafi cikin kwando Tana cikin wannan hali ramlat ta same tace "Hajiya lafiya?, a jiyar zuciya tayi tace "Ba komai, Sopa ta samu ta zauna ta rungume pillow cases tace "Hajiya yarinyar nan bata da kirki ɗaƙin kwanan baki ta kai mu tun wancan satin nake so in Miki magana to kinyi tafi London a duba lafiyar ki, Dafa kanta tayi tace "Kice mata ta baku keys ɗin kusa da ɗakinta, "To, Tashi tayi ta bar gun ta nufi ɗakin yusrah handle ɗin ta murɗa ta jishi gam ta rufe tsaki ta ja ta nufi garden domin tafi kyauta zaton tana can haseena ce ta tawo tana jin waƙa tana ganin ramlat ta bangaje ta tace "Tsohuwar guzuma yara yake nema irin mu, A fusace tayo kanta zata dake ta sauke hannu tayi ganin wanda ba suyi zato ba wani irin kyau yayi yana sanye da brown ɗin shadda gezna an mai aiki da milk ɗin zare yasa hula zanna buƙar ta ƙalmin ƙafar sa milk colour ne yayi wani irin fari saboda ya dan rame saboda kwana biyu ko ishashshan bacci baya samu gashi a na dab da zabe ga shi wannan auran da zaiyi yayi shine dan manufa amma besan ta wacce fuska Hajiya zata ɗauke shi ba domin ko a idanuwanta yana gano tsanar binta a idonta cikin izza yake takuwa floor kallo ɗaya za kai mai kasan namijin duniya ne ga ilimi ga kudi sajan fusƙarsa ya kwanta lub lub yaji duk abin da su ramlat sukai sai dai be nuna musu ya ji ba sai ma kare haɗe fuskar sa da yayi Duk kan su ɗur ƙusawa sukai suka gaishe shi Ciki ciki ya amsa ya shiga ci hajiya Turai na ganin sa ta miƙe ƙasa yayi da idanuwansa ya ɗur ƙasa yace "Hajiya barka da dare na sameki lafiya?, sassauta zuciyar ta tayi ganin ya koma mata mahaifinsa sak tace "Yauwa mu'azzam ashe daman baka da tunani ka rasa wa zaka aura sai shegiya yar tiktok wacce ta fito idon duniya ta yi maka ƙazafi mu'azzam me kake so jama'a suce su shaida maganar da ta faɗa ita ta tsoratar da kai har ka aure ta saboda gudun tunuwar a sirin ka , Ƙasa yayi da idanuwan sa cikin deep voice ɗinsa wacce ƙara ra ta nunawa rauninsa a gun mahaifiyar sa ya kuma so ta fahimce shi yace "Hajiya ban yi haka dan tozar ki ba ko in tozar ta Kai na ba a'a na yi shine da manufa bani da hanyar da zan azabtar da ita sai ta wannan yanzu idon jama'a a kai na yake komai nayi za'a ce ban yi adalci ba duk da bana tsoron maganar mutane Sannan kamar nayi jahadi ne ba zata ƙara aika ta maka mancin sa ba zata kuma nutsu sannan tare suke da mai tasa a lokacin da a ka harbe mahaifina su mai tasa suna gun me isa ba a haɗa da su ba alamun kisan an yi shine da tsari daman shi a ke nema wannan dalili ne yasa na shiga siyasa me zanyi da mulki bayan ba abin da Ubangiji be bani ba in na barta tare da mai tasa zata ci gaba da yimin ƙazafi har al'umma su y.arda wa zai bani ƙuri'ar sa bacin bani da aure wata ƙila zata iya sanin wani sirrin su kinga ansami sauƙin binkice ko, Jikin ta a sanyaye ta sami gu ta zauna tace "Na yarda Allah ya temake ka kullum da mutuwar mahaifin ka nake kwana nake tashi sannan har abada bazan sota ba kuma dole ka ƙara aure in komai ya lafa zan nemo maka yarinya yar munci yar gidan manya ka aura bazan taɓa haɗa jini da shegiya ba ban hanaka kusantar ta ba amma dole a gwadata ɗan nasan baza ta rasa bin maza ba bata da wasu a bokanai sai maza , Hamdalah yayi a ransa ya godewa Ubangiji yace "To Hajiya nan ya kwashe komai ya faɗa mata ya kara da cewa gobe za aje gun kahunta , Allah yayi albarka tace Ameen tashi yayi yace "Ni zan shiga ciki , ɗa gowar da zai yi yaga mutum ya yi sauri ya koma dan murmushi yayi wato yaran nan laɓe ke yi musu gaban labulan yaje yana sane ya murza ƙafar ta iya a zaba taji bata san lokacin da ta ƙwalla ƙara ba ta fito hucewa yayi kamar bashi ya aikata haka ba *CI GABAN BINTA YAR JAGALIYA* Jifan gafiyar ɓedu *Ba tsuntsu ba tsarki* By Oum Yasmeen Book two Ban hanaki karanta littafi na ba amma kinsan Allah baya yafe hakkin wani a kan wani typing a kwai huya ki daure ki mallaki naki ba kuɗi mai yawa 300 kacal Ki yiwa Allah da Manzonsa ƙarki karantan littafina in kinsa baki siya ba sai kujera sai an gama littafi ku dinga ƙaramar murya a temaka a baku Dan Allah duk wacce ta siya ta ruƙe amana ƙarta fitarmin da book ɗina Wasu hawaye ne suka dinga xubuwa haseena ga farcan ƙafarta da tasa ya lume a gaskiya yaya mugune na ƙarshe bashi da imani yanzu me zata cewa hajiya ba abin da taji ban da huya da tasha tashi tayi tana ɗingisa ƙafar ta Washe gari Da sassafe Binta su ka fita unguwa ita da rufaida a cikin motar ta zata siyar da motar ta ta biya kuɗin ta fiya Makka domin kuɗin hannunta ya kare ba zai isa zata cika ta kaiwa wanda rufaida ta haɗa ta dashi duk abin nan da ake kahu labahani be sani ba kuma bata da niyar faɗamai sai de ya shafa yaji ba ita cikin Sa'a aka siyeta miliyan ɗaya zata haɗa da dubu dari da hamsin na wajanta ta bashi domin a jiya da rufaida ta haɗata dashi yace komai za'a bata har da gun Zama sai taga mahaifinta sannan ta dawo tayi murna sosai rufaida ta dafata tace "Sister tunanin me kike?, murmushi tayi har beautiful point ɗin ta ya lutsai tace "Wallahi farin ciki nake burina yana gabda cika , A jiyar zuciya tayi tace "Har naji dadi amma ai ban dake za ai zaɓe ko?" Hmmm wanne zaɓe ga abin da yafi zaɓe kin ga wallahi gaba na har waɗuwa yake in na kalli poster ɗin mutumin nan nan fa ofishin jam'i yar sune na ƙaramar hukumar gamji Msw ke wallahi kina da ban haushi bara in tarar mana abin hawa muje mukai kuɗin nan ai kafin ta rufe baki an fusge jakar hàññun ta ihu suka sa suna bin mutumin dake babur tuni ya ɓacewa ganin su wasu zafafan hawayene ya zubo mata ta dubi rufaida tace "Rufaida kin ga irin tawa kaddarar ko wayyo Allah na ka kawo min dauki , Wani dutsai ta samu ta zauna tace "Kawata ki haƙuri Allah ya mayar miki da alkhairi wallahi ban tabbatar da maganar mutane ba da suke cewa hanyar nan ba kyau sai yanzu tashi mu tafi gida azahar ta kusa , Jiki a sanyaye ta tashi tace "Rufaida bani da kuɗin komawa gida da, Ƙar ki damu mu tafi a ƙafa nima bani da ko ƙarfanfana Cikin sauri ta buɗe jaƙar ta tace bara in duba account ɗina ko ina da kuɗi dan dane dane ta shi ga yi buɗa hasƙen wayar ta tayi sosai domin ta tabbatar abin da idon ta ya gani naira hamsim ce da kabo shida aciki bata san lokacin da tace "Innalillahi wa'inna'laihir raji'un Allah ka kawomin ɗauki rufaida sai da naci miki su toron ta account ɗina kikace mu kai mai hannu da hannu shikkenan ai gashi nan kin jajamin zo mu tafi , Wayar ta ce tayi ƙara cikin sauri ta ɗaga ganin mai kiran tace "Okay gani nan zuwa , Duban bintu tayi tace "Dan Allah Binta ki haƙuri yanzun nan ƙanwar mamana ta kirani tana asibitin hayan daro nan kusa zanji bata da lafiya, Cikin tashin hankali bintu take kallon ta tace "Tafiya zaki ki barni a cikin wannan halin da nake ciki?, Haba binta haihuwa zata yi fa da ƙƴar take min magana kin ga sai an jima tayi gaba abinta ba yarda Binta ta iya tayi gaba tafiya tayi mai nisa tuƙun na ta zo wajejan layin su gaban wani tuƙa tuƙa ta tsaya ta wanke ƙafafuwanta da sukai fututu ta gyara mayafin ta ta shiga layin da ta sai gida gate ɗin gidan ta nufa zata buɗe taji an mata magana tsayawa tayi ta jiyo tace "Malam lafiya zaka miƙo min taƙarda me zanyi da ita ba bayanin komai ?, Babur ɗin sa ya kafe yace "Ta biyan kuɗi ce, Zuciyar ta ce ta kawo huya tace "Sai naci abu ta kazar uban kuɗin kai kalleni da kyau nayi maka kama da wacce za kaiwa wannan shashancin to ni ba kuɗin da ake bina wallahi ka barnan ko in naɗa maka doka danni faɗa da namiji ba abin nema bane a guna, Sunana jabir Kabir lauya dake karbar kuɗin hayar gidan nan ya sauran kwana biyu kuɗin ki ya ƙare ga wannan ta ƙardar ta biyan kuɗice kije ofishin mai kula da manya mayan gidaje da rumfuna ki biya Turus tayi lallai rufaida ta cika maci amana daman haya ta ƙarɓar mata ba gida ta saya mata ba ya hun baƙin tane ya kafe da ƙƴar ta sa hannu ta amshi ta ƙardar tace "Okay zan je in biya , Fasa shiga gidan tayi ta fara tafiya rike da taƙarda asibitin da ta ce mata zata nan yanzu ta nufa ta kiran ta tashi ga yi ba aɗaga ba ƙarshe ma sai aka kashe wayar sosai zuciyar ta ta zo har huya ga rana da ta sha tafiya ta ke yi kamar zata waɗi tun safe ba abin da taci sai ruwan shayin da tasha ƙofar a gate ɗin a sibitin ta nufa kai tsaye inda ake amsar masu haihuwa yawo ta ɗin ga yi ko mai kamar rufaida bata gani ba nan ta tsaya tana mai da numfashi anya kuwa satar kuɗin nan da akai banda sa hannun ta nan komai ya dawo mata tambas haɗa baki a Kai da ita in tasan wata ai bata san wata ba gidan su zani wallahi sai nayi mata rashin mutunci Wannan kenan Barar rajewa yayi a mota yana shan a.c a zuciyarsa kuwa cewa yake lallai kuɗi yayi a rayuwa duk wannan ranar be San a nayi ba gaban wani ɗurƙushashshan gida yace so tsaya duk almajirai a zaune suna akaratu malam Umar yana zaune yana rubutu fitowa yayi na gyara rigar bararsa sallamar da yayi ne ya ɗau hankalin malam Umar ya ɗago yace "Wa'alaika salam barka da zuwa , Kahu labahani yace "Malam ko baka gane ni bane nine nazo da magana me mahimmanci ne?, Gyara hiramin sa yayi annurin fusƙarsa ya ɗauke yace "Ko muryar ka naji sai na ganeta ɓalle inga wannan fusƙarka da son a bin duniya yayi mata ƙawa, Ranƙwafuwa yayi yace "Kai a hankula ina tafi ne da surukan mu binta ce zatai aure , Tuni kamilal fusƙarsa ta cika da annuri yace "Masha Allah shi go da su kallo almajiran sa yayi yace su bashi guri farin ciki ya mamaye shi Allah ne kade yasan irin farin cikin da yake ciki binta ta shiryu tun da har zatai aure sun bashi mahimmanci ne har suka sako da shi a maganar auran nata , Ajjiye allo sukai suka fita a rumfar karatun nasu Alhaji mansur da muzabfar da mu'azzam suka shigo cikin rumfar sallama sukai Amsawa yayi cikin sakin fuska yace "Barkan ku da zuwa ga waje ku zauna, Yauwa su kace suka zauna Alhaji mansur yace "Abin da ke tafe da mu mun zo nemawa ɗana auran yar wajan ka binta sunana Alhaji mansur mu'azzam kura , Hammadalah yayi yace "Ina ɗan da zai aure ta ?, Gani muazzam yace Sosai malam yaga kimar sa da nutsuwarsa da kwarjininsa yace "Tana son ka mece sana'ar ka ?, Ƙasa yayi da kansa yace Ni ɗan kasuwane sannan ɗan siyasa nan ya kwashe komai ya faɗa mai amma ya ɓoye manufar auran Ƙar ku damu na baka auran binta nan suka bada sadaki yace ba sai yayi lefeba ya shiga masallaci a Ka daura auran mu'azzam Bilal mu'azzam Kura da Fatima Umar akan sadaki dubu shidda inda shedo suka tabbatar sai da aka dau komai a video domin nuna mata malam Umar yace "Ɗana alkawarin ɗaya za kai min dan girman Allah da manzon sa ka ruƙe binta amanah ƙarka cutar da ita marainiya ce ba uwa ba uba bata da gata sai Allah babu saki a tsakanin ku ka gyara mata rayuwa, Nauyin mutumin ne ya kama shi ba zai iya yi mai musu ba yace "Insha Allah na ɗauka , Ungo sadakinta ka bata da hannunka sannan wannan kuɗin da kuka bani na gode bazan amsaba sarai ya gane fusƙar mu'azzam shene meneman takarar shugaban ƙasa Amsa yayi yasa aljihu yace "Dan Allah ka amsa kyauta muka baka , Dubu goma ya zara a cikin dami biyun kuɗin da ya bashi yace Ungo wannan wayan nan sun isheni na gode Allah yayi albarka Bayar da suka iya suka amsa kahu labahani ji yayi kamar ya shaƙe dan uwan nasa sosai suka yaba da halin malam Umar saɓanin na labahani wanda son kuɗi da duniya ne a gaban sa be damu da kuɗin sa ba sai da yayi binkice tukunna ya yarda ya daura auran hawa mota sukai suka tafi daman tun da safe a Ka yiwa labahani komai na shirye shiryan tafiyar sa Makka da kuɗinsa a kofar gidan sa a ka sauke shi sauke shi suka juya kura estate Allah ya isa kika karanta min littafi baki biya ba typing a kwai huya Wannan kenan Ko sallama batayi ba ta kutsa kanta cikin gidan Hadiza Hadiza Hadiza Cikin sauri mahaifiyar rufaida ta fito cikin mamaki take kallon Binta tace "Binta yau ni kike kira da Hadiza ba sakayawa?, wani banzan kallo ta watsawa mahaifiyar rufaida tace "Ƙarya nayi ba sunan ki Hadiza ba maciya amana ina rufaida wallahi sai ta biyani kuɗi na tun da ku baku da mutunci matsiyata?, ɗaurita mahaifiyar rufaida ta gyara tace "Au dan taci wayan nan matsiyatan kuɗin kuɗin kazafi ai daman su basa albarka fitar min daga gida , Ai kafin ta ƙarasa Binta ta rarumi muciya ta buga mata a gadon baya tace "In tazo ta ga saƙona kafin ni in dawo , Wayyo Allah maƙota ku temaka min ku temaka min Wata uwar dariya Binta ta saki tace "Karo dani ba dadi yasin idona idon rufaida sai na mata abin da har ta mutu baza manta dani ba, Tana durƙushe tace "Ai kida ganin rufaida sai a lahira domin yanzu nasan ta isa inda takai , Ganin kamar bata ji a jikin taba yasa ta ƙara dauƙar taɓarya ta dai daici ƙafafunta ta maka mata Ƙara taƙwallah nan maƙotanta suka shigo cikin makirci Binta tace "Mama lafiya me ya sameki?, Jikin moƙotanta ne ya yayi sanyi Domin su ba susan abin da take nufi ba sunde ganta a kwance maga shiyan wata daga ciki ce tace babar rufaida lafiya ƙarar huya ta saki tace "Wannan can wallahi ita ta naɗan duka , Zaro ido Binta tayi ta share hawaye tace "Na shiga ukku rashin lafiyar take har ta kai haka yanzun nan rufaida ta kirani tace jikin mamanta ba lafiya ciwon hauka ke damunta inzo ita tayi tafiya, Salati suka saki tuni wajan aka fara jimami Wallahi ƙarya take lafiya ta qalau Matsawa Binta tayi irin tana tsoron Hadiza tace "A kira mazan waje su ɗaure ta tun kafin ta fara duka , A guje ta yo Kan binta ai kuwa ta fita nan mutane suka yarda da maganar Binta gudu take da ƙƴar a ka sami wanda zai ɗaure ta ajikin bishiyar lahinsu Hadiza kuka take tana cewa "Wallahi ina da hankali Binta kin cika me maƙirci , Ba wanda ya kula ta Wannan kenan Hajiyan taura Alhaji mansur sai mabiyin sa mahaifin Ramlah Alhaji Nura sai Hajiya kubura mahaifiyar haseena tuni ƴa'ƴa da jikoki suka hallah a taron muzabfar Alhaji mu'azzam da azzam da sauran yan family ɗin Alhaji mu'azzam ya fara buɗe taro da addu'a yace "Ina me bawa Kowa haƙuri wani dan gajeren al'amari da ya faru a yau juma'a na ɗaurawa mu'azzam Bilal mu'azzam kura aure kuyi haƙuri sakama ƙon rashin sanar da ku muma ya zomana ɓakatatan ne ba zato sai dai ku mai addu'a Allah ya basu zaman lafiya bana son wani gutsiri tsoma a yau amaryarsa zata tare , Nan ran Alhaji Nura ya ɓaci kowa yasan Ramlah na mutuwar son azzam Amma saboda wariyar launin fata an zagaye an mai aure tuni mahaifiyar haseena ta ɓata fuska dan anga mahaifiyar su ta mutu shi yasa baffa ke yin abinda ya ga dama ai bata sunƙe da lamarin nasa ba sai taji yace "Duk wani jika da yake gidan nan to dole ne nan da wata biyu bayan anyi zaɓe kowa hankalin sa ya kwanta su fitar da miji su aure barin Ramlah da haseena na gaji da yawon su kai Muhsin Ramadan wallahi ku kiyaye ni na baku wasu watan Ni inga kun fito da matar aure, Ran Hajiya kairiyyah ne ya ɓaci tace "Tun da anyiwa ɗan gold aure ai dole ka tarkata kan ƴa'ƴa da jikoki ka ce su fitar da miji , Wani banzan kallo yayi mata yace "Hajiya kairiyyah ki iya kalaman ki in ba haka ba zaki dana sani, Murmushi tayi wanda yafi kuka ciwo ta fita daga ɗakin taro yace Kowa zai iya tafiya nan kowa ya fita jiki a sanyaye jidda kuwa tana zuwa ɗakin ta ta saka kuka yau wanda take so zai tare da wata matar ba ita ba Wannan kenan Azzam wa zai ɗauko wacce yarinyar naso insa a ɗauko ta saidai yanzu ance ta dena zuwa club kaga da abin yayi mana sauƙi ko ba idon mutane a lokacin Gaban sa ya waɗi domin shi ya manta da zancan binta yace "Malam Musa zai tsaya abayan gidan su inta fito shi da su Joseph sai su rutsata ta shiga Mota sai a shaƙa mata Powder a Kai ta gidana dake laimon kafin musan yarda za ai bayan an gama zaɓe , A jiyar zuciya yayi yace "To Allah ya temake mu, Ameen yace ya tashi ya nufi shashin muzabfar a bakin gate ya haɗu da shi yace "Dan halak yanzu gunka zani fa , Ai gani nan na zo ko Hakane ango Harara ya watsai mai yace Wallahi ka kiyaye Ni kasan ko a makaranta ni ke naɗa maka duka yanzu ƙuruciya zata tashi fa Dariya yayi yace "Ai mun girma tunda kai aure Ni ina da baby mushi ga ciki, Banza yayi mai suka shi ga aguje mufeeda ta tawo gun sa tace "Uncle azzam congratulations 🎉 , Daga yarinyar sama yayi sosai ta shiga dariya tace Uncle yaushe zaka kaini gun antyna Cikin sauri ya dubi Mubaraka Ƙasa tayi da idonta tace "Sannu da zuwa Allah ya sanya alkhairi, Ameen ya ce Ya sami gu ya zauna ya ɗora mufeeda a cinyar sa zance yarinyar ta shiga yi mai yayin da Mubaraka ta ɗauko lemo da ruwa ta ƙawo mai da gashashshan nama ta ɗora a kan Center table ta bar gun Muzabfar yace "Babyn jike gun momin ki ki zauna ki ƙƴale uncle ɗinki ya ci abinci, "To daddy ta bar gun , Wanna kenan *CI GABAN BINTA YAR JAGALIYA* Jifan gafiyar ɓedu *Ba tsuntsu ba tsarki* By Oum Yasmeen Na kammalah book 2 ki ɗaure ki mallaki naki opay bank 8141785374 AMINA ALHASAN MUHAMMAD ki toro shidarki ta wannan number 09061890481 Ban hanaki karanta littafi na ba amma kinsan Allah baya yafe hakkin wani a kan wani typing a kwai huya ki daure ki mallaki naki ba kuɗi mai yawa 300 kacal Ki yiwa Allah da Manzonsa ƙarki karantan littafina in kinsa baki siya ba sai kujera sai an gama littafi ku dinga ƙaramar murya a temaka a baku Ki karanta halalinki Dan Allah duk wacce ta siya ta ruƙe amana ƙarta fitarmin da book ɗina https://chat.whatsapp.com/Fu2P8PebrYYAXRI3z0vvXh Ƙafafuwan ta fututu ta dawo hanyar gida domin har gidan gwamnati taje ga wata irin yar gajiya da ta kwaso ta dawo da alƙawari kala kala da gwamna yayi mata indai har ya sami shugaban kasa kaso cas'sa'in na cikin damuwar kuɗin ta ya rago domin tasan zata sami ninƙinsu unguwar tayi shiru baka jin motsin komai kowa ya tafi ya kwanta ga wani irin duhu da garin yayi alamace da ke nuna damuna ta shigo daman yau anyi zafi ga rana bishiyoyi sai lumshi suke suna bada wata iriyar iska tsiƙar jikin ta har tashi take saboda irin sanyin da take ji hasƙen farin wata sai kaɗan sauri ta ƙara dan ta lura ruwa yana gab da kecewa wata baƙar mota ce ta sha gaban ta ƙaucewa tayi ta ci gaba da tafiya ta ruƙe jaƙarta da kyau ji tayi yinwar da take ji babu ita ta ɗaga ƙafafuwanta ta fara sauri ji tayi an saka mata ƙarfe a bayan ta tana kyautata zaton bindiga ce aikuwa ilai ita ce ɗaga ƙafafuwan ta tayi zata zuba gudu nan yace "Ƙina ƙara motsi sai na fasa ƙwaƙwalwar ki da alburushi , Jikin tane ya hau mazari ta ɗaga hannu wanta sama ashe bashi kaɗai bane zaratan sojojine majiya ƙarfi su shidda sun zaga yeta ɗayan yace "In kina son ki da lafiya shiga cikin mota , Ba yarda ta iya bakinta ya mutu bata da wani sauran zaɓi da ya huce ta bishisu gidan baya suka buɗe mata ta shiga inda mutum biyu suka sata atsakiya ga wasu irin shigun bindugu a hannun su sauran suka shiga gaba sai wani tsoho driver ba damar ihu domin duk ihun da za tayi ba me jinta wasu zafafan hawaye ne suka shiga zubo mata yawa ansaki fanfo wani abu ɗayan ya ɗauko ya fesa mata bata ƙara sanin inda kanta yake ba baƙin hanya suka tsaya wata mota ci ta tsaya fara ƙal da ita wani matashine me jini a jika yana sanye da farar t-shirt da jeans baƙi ga hula p-cap yasa ya sa face mark ba zaka iya gane ko wane ba ga baki ɗayan su suka fito suna sara mai amsar key ɗin motar yayi ya basu nasa ya buɗe ya shiga a guje driver ya ja ya bar gun su kuma suka shiga cikin farar motar suka bar dajin Ƙarfe 7:38 na safiya Idon ta wani irin nauyi yayi da ƙƴar take ɓuɗe shi za bura tayi ta yaye lallausan bargon da aka lunluɓeta kallon ɗakin ta shiga yi anya kuwa duk abin da ya faru ba mafarki take ba murza idonta tayi ƙara ta ƙwallah ta tashi da sauri ta sauka daga luxury bed ɗin komai na ɗakin farine harta laburayan fararene iska sai ƙada su take ga ɗan hasƙen da ya shigo ta taga cikin sauri ta nufi ƙofa jinta tayi gam a rufe nufar taga tayi ta leƙa Ware manyan idanuwanta tayi wasu irin gine gine ta gani masu kyau da tsari ga jami'an tsaro sai zurga zurga suke a gidan saƙin labulan tayi ta shiga raira kuka me ban tausayi tambas tasan Ubangiji ne ya kamata domin baya barin hakkin wani a jikin wani ko da gine ginan da ta gani ta shaida ba a ƙasar nan take ba ko tana babban birnin kura wato laimon tashi tayi ta shiga bugu ƙofar ba kakƙautawa bata san an buɗe kofar ba ta cigaba da bugu bata ankara ba ta jita kane kane a jikin mutum a razane ta ja da baya manyan idanuwanta ta buɗe gabanta ya yanke ya waɗi ganin wake gabanta yana sanye da wando three quarter ba riga ga wani irin yalwatatcan gashi a kwance a faffaɗan kirjinsa jikin sa duk a mulɗe yawa dan danbe fatar sa har ɗaukan ido take saboda hasƙenta ga ƙananun gargasa lub lub ra ƙuɓewa tayi jikin ta ya saɓi rawa wani irin shock ta shiga bata taɓa ganin namiji a haka ba kuma irin wannan maji ƙarfi iya dana sani yau ta shege ta ƙara haɗa fuska yayi sexy eyes ɗin sa ya ware su tar a kanta kafuwanta ya duba wanda sukai fututu ya dubi zanin gadon sa duk yayi ɗauɗa yace "Ke wacce irin wawuya ce wacce bata san ciwon ƙanta ba ina ƙwanci ina damuna jibi ƙafafun ki to wallahi sai kin wanke min zani kuma da hannu ba da washing machine ba, Kuka ta saki ta ɗurƙusa ta haɗa hannu biyu tace "Dan girman Allah ka mai dani gida kai haƙuri wallahi ni ba yar iska bace ƙar ka cuce rayuwa ta wallahi nayi nadamar a bin da nayi maka tun ba yau ba wallahi bazan iya wanke wannan blanket ɗin ba, Dariya ya saki har sherarrun haƙuransa farare tas suka bayyana Shagala tayi tana kallon sa saboda wani irin kyau da yayi Lura da irin kallon da take mai ya haɗe rai yace "Keee mayyar maza ya zaki sa duda abin da keke so shi zan baki a sanga batare da kin biyani ba ko kin sha wahalar zuwa club kuma wallahi tun huri ki ɗauki wannan bargon ki wanke min ƙaaaazaaama ya ja ƙarshan , Dan Allah kai haƙuri ka mai dani inda ka dauko ni wata loca ya buɗe ya ciro wasu miƙakƙun kudi yan dubu dubu ya watsa mata yace "Ga sadaƙin ki auran ki nayi , Ihu ta zunduma ta zube a ƙasa tana kuka tace "Wallahi ƙarya kake , Ta kuwa ya fara har inda take ganin ya kusan cin mata idanuwansa sunyi wani irin ja haka fusƙarsa A gi gice ta tashi ta fara ja da baya yana bin ta har ta kai bango bata da hanya guduwa saboda ƙawanyar da yayi mata da hannayansa ko wannan su yana iya jiyo numfashin ɗan uwansa yace .........✍🏻 "Ki iya kalaman ki ƙar kisani inyi abin da ban niya ba ki tattara kuɗin nan tun kafin ranki ya ɓaci wankin da nace kiyi ƙar kiyi ki bari indawo in same ki baki yi ba , Wani marayan kuka ta saki tace "Ina jaka ta ɗan Allah ka sakeni in tafiya ta?, Har yaje bakin ƙofa ya tsaya cak yace "Zo ki murɗeni ki kwata ki saranki kin shigo gidan nan kenan zama daram, zaman da ɓaro tayi a bakin gado ta gumi tayi ta rasa ta ƙameme tunanin da zatayi duniyar ta yi mata zafi jin alamu ƙarar kofa da sauri ta tashi mulɗewa tayi taji abuɗe yawa ba wayayyiba sosai ta shagala da kallon floor an kashe dukiya wajan tsara shi floor biyu ne a haɗe sai aka raba shi da water bubble partition sai kawo huta yake kala kala ga tamkeƙen pic ɗinsa yawa zai magana a kusa da dining room shida mahaifinsa sun rugume juna suna murmushi jin taku tayi da sauri ta juyo ya sha yadi fari sosai yayi kyau ya fito a babban mutum da kamalal sa ta fito kwar jinin sa ya cika mata ido niya tayi ta cimai mutunci ta zage shi ko zai sake ta amma ina ta kasa yawa yayi mata asiri tayi ƙasa da kai ta baza ta ma iya kallon sa ba ta ja baya ƙwallah ta tarar mata a ido tace "Dan Allah da Manzon sa ka fitar hannunsa ya zuba a aljihu cikin deep voice ɗinsa yace "Ga abinci nan a dining ki ci daga yau na canza wa me min abinci ke zaki ɗin ga yi ba abin da babu a store ƙar kiyi gigin fita daga gidan nan in kuma ƙinƙi gaki ga hanya nan hmmmm ya saki murmushi na gefen baki ya wuce, Turuss kalaman sa na ƙarshe sun ɗaga mata hankali dafa wata luxury s sofa tayi jiri na ɗi banta tuni numfashin ta yake kai wa da komowa ta tsinemai yafi cikin kwando ganin ba sarki sai Allah yasa ta meke ta nufi dining wasu hadaddun luxury warmers ne yan gidan stainless steel vacuum sai ɗaukar ido suke yawa an haɗa da sirkin gold na farko dambum cuscus yaci kayan lambu da hantar rago ɗanyan ta buɗe farfesun kazane yaci kayan kamshi kadan ta zuba ta buɗe na alemo da lemon kwakwa ne sai na mango juice tissue zara ta goge bakinta ta koma ɗakin da tafito zanin gadon ta ƙalla fasa wankewa tayi ta shiga toilet shagala tayi da kallon sa ta yarda da komai na azzam me kyaune mayukan gyaran jiki ta gani kala kala yawa mace ga wani dugun glass anzube towel set farare tas da su ko wanne da amfaninsa cire duguwar rigar ta tayi cikin bathtub shiga da yake ta gama haɗa komai ruwan sai kamshin turaran wanka yake gamawa tayi ta ɗauki towel me dan girma ta daura iya gwiwa abar busar da kai ta dauko ta busar da kanta ɗaukan rigar ta tayi ta sa a washing machine bayan ya gama wanke wa bata jira ya busar da ita ba ta ɗauka ta shanya zanin gadon ta yaye ta ɗauko wani a cabinet ɗin toilet ta canza tasa wannan a Landry basket curtain ɗin ta ja ta rafe ko ina saboda wata iska da ta taso tuni aka ɗauke huta solama basu kunnata ba wata irin iska ake mehaɗe da walkiya hawa kan gado tayi ta ta kure Wanna kenan "Mu'azzam ka kai ta gwajin da nace ka kai ta ?, Aa yau nayiwa Dr nazeer magana zai zo Kofin hannuta ta ajjiye tace "Okay , Hajiya ni bara in tafi Allah ya tare Ameen ya ce ya fita a main floor ya tarar da su Ramlah yawa an musu mutuwa sunyi jigum jigum suna jin takunsa ko wacce ta zuba mai ido yawa me shirin gano wani abun suna ganin ya ƙaraso kusa da su ko wacce ta ɗauke idonta suka gaisheshi cikin kissa haseena tace "Yaya zan bika inga anty zarah , Ɗagowa yayi ya kalli ta domin shi wallahi ya manta da zancan ta ya manta da yabar mutum a gidan nan yawa ne ciwon baki yace "Ba yanzu ba ya wuce warsa cikin sauri domin ruwa ya kece yawa da baƙin ƙwarya cikin sauri ya shiga mota malam musa ya jashi suka tafi dake nan kusa da sune nan da nan suka isa sojojin da suke mai gadi suna jin horn ɗinsa suka buɗe da yake duk ruwan da za ai ko iska basa matsawa har gaban bangaren sa aka kaisa ya shiga floor ƙasa ba kowa kai tsaye bene ya hau ya shiga ɗakinsa ya shirya ya fito floor ƙasa ba kowa kai tsaye bene ya hau ya shiga ɗakinsa ya shirya ya fito Cikin ƙanan kaya iya kyau yayi kyau yawa wani balarabin Turkiyya wandon jikin sa dark ash t-shirt ɗin baƙa anyi rubutu a jikin ta ansa gallery depth da fari kitchen ya nufa haɗa coffee yayi wanda ya ji kayan ƙamashi sai da ya matsa lemon tsami shidda yafito ko sugar besa ba a kitchen ɗin ya zauna yaja kujera ya fara sha a hankali yawa me koyar cin abinci tashi yayi ya dauko system ɗinsa ya fara duba aikin da akai yau kacokan ya maida hankalinsa kan system ɗin jin ihu yayi da sauri ya tashi ya fito ya nufi ɗakinta murɗawa yayi ya shiga ya ƙunna filar wayar sa yace "Lafiya ?, taso wa tayi tamanta da yanayin da take ciki ta rungume shi ta saki kuka so yake ya hanata amma ina ya kasa yawa anruƙeshi nunamai ƙasan ɗakinta take tana kuka wani kumurcin mucijine yana fasa kai yayi ƙasu da sauri ya ɗauketa cak yawa wata yar baby suka fito waya yayi an danan sojojin suka zo suka shiga ɗakin kunyace ta kama shi gani duk ta maƙalƙaleshi Allah yasa ya ƙauce da ita basu ganta ba ganin irin kayan da yake jikinta fita sukai da shi ya dawo floor yace "Ki sauka tunda kinga sun fita da shi ko , Yawa wata yarinya ta shagwaɓe baby face ɗin ta tace "Uhmm dan Allah ka fitar dani daga nani gidan, Kafe tayi da sexy eyes ɗinsa shi kansa besan cewa abin da tayi zai mai saurin illah irin haka ba kallon fatar ta yake tana wani sheƙi gata ba fara ba amma tana da wani sirƙin kala me ɗaukar hankali ko dan shi a tsarinsa ba yason farar mace ne owo uwa uba shagwaɓar da tayi ta tafi dashi daƙƴar ya iya buɗar baki yace "To sauka ƙarki ƙarya ni, Ƙunya ce ta kamata ta gyara ɗaurin towel ɗin jikin ta tace "Kayana na wanke ko zaka shiga ka ɗauko min ?, Girgiza mata kai yayi yawa ƙaramin yaro ya bar gun ganin yana nema ya shiga ɗaki ya barta ta zuba a guje ta bishi haɗa girar sama yayi da ta ƙasa yace "Me zan miki kika biyoni?, Wasa ta fara yi da zarazaran yatsunta tace "Ba zan iya zama Ni kade ba, Bata kula da yanayin da yake ciki ba ta ɗago ta kalle shi ganin yayi mata shiru idonsa yayi yayi ja cikin rashin sanin ta ƙameme me ya same shi tace "Idonka ne ke ciwo ?, Be bata amsa ba sai hanya da ya bata ganin kamar baya son magana Bata da wata sauran dabara ban da ta bishi ta shiga komai na ɗakin up white ne zama tayi a wani lilo kusa da wata ƙatuwar taga ta cinye rabin bangon ɗakin ga table a tsakiya ga ta ƙardunsa da jaridu tanƙwashe kafuwa tayi ta ɗauki wata jarida ta soma karantawa ta shagala gurin karanta jaridar har bata san ya shiga ban ɗaki yayi wanka ya fito jaridar wani barabene shine yanzu me jiran gado shi ake kyautata zaton king abdulyasar bin Omar zai sauka ya bashi ji tayi an fusge jaridar da sauri ta kalle shi fusƙarsa ba alamun rahama yace "Wa ya saki ki ɗauƙar min, Tsoransane ya shigeta bata taɓa ganin mutum irinsa ba yawa wahainiya lokaci ƙalilan yacanza siraran labɓanta ta ɗaga tace "Ba kowa, Okay wannan shi ne last warning da zan miki ƙarki ƙara ganin wani abu nawa ki ɗauka har ki karanta ungu rigar nan ki saka ya miƙo mata jallabiyarsa Amsa tayi ta shiga toilet ta sa ta fito tana rurruƙeta tayi mata yawa ga Brest ɗinta ba bra ganin ana gano komai tana da buɗadɗan huya sai ta yafa towel ajikinta tasami wani gurin can ta rabe da yake har sallar isha yayi kafin ya shiga gidan su huta aka kawo ya kashe fitilar wayar sa wayar sa ya ɗauka yayi danne danne ko minti ɗaya beba aka ɗauak yace Hello joshiwa Cikin girmamawa yace Goodnight sir how are you "Very well, " Me yasami solar gidan nan naga an ɗauke huta ba akunna ba ?, Wallahi ta sami matsala ne bayan fitar ka na kiraka ba Kai picking ba Samin gu yayi ya zauna yace "Me isa ba kaimin text ba ?, Ranka yadade kai haƙuri wallahi nasha'afane Okay in irin haka ta faru kawe ka kira me gyara gobe ka kira Company su duba matsalar "To sir, Kashe wayar yayi ya zauna ya ɗora ƙafa daya ƙan daya yana girgizwa yace "Baki wanke blanket ɗin nan ba to wallahi gobe ki haɗa da riga ta ki wanke koma sauran inji tana tsami, Shiru tayi mai domin ita yanzu tsoro yake bata daman hausawa sunce ɗan hakkin da ka raina shike tsole maka ido ta haɗa kanta da gwiwa abin duniya duk ya ishe ta gashi da ta shiga toilet taga period ɗinta tazo Kallonta yayi yace "Jeki kitchen ki ɗauko min system ɗina , Zaro dara daran idanuwanta tayi tace "Bazan iya ba , Ɗago fusƙarsa yayi sukai 4eyes ɗaukenata tayi domin fusƙarsa ko ɗugun annuri babu yace "Aikin iya fita da tsakiyar dare ko tsoro baƙƴaji baƙƴa gudun kina kan hanyar ki ta tafiya ki mutu ko kina can ko da yake sana'a kike zuwa ko gobe Dr zai zo ya duba lafiyar ki domin ban yarda da keba kina karama dake kin jefa kanki cikin wahala ban aureki dan inyi zaman aure da keba sai don in koya miki hankali, Kuka ta shiga rerawa cikin matsanancin tashin hankali zuciyarta sai xugi take tace "Wallahi ba wanda zai dubani ni ba yar iska bace kuma da kake cewa ba zaman aure za kai da niba to kasakeni natsaneka banason ka kuma wallahi wannan buɗurcin ƙwalelanka yafi ƙarfinka, Yawa wani mahimwacin zaki yayi kanta tashi tayi a furgice yace "Ki kiyaye kalaman ki ko wallahi ki ƙarki sani inyi abin da banniya ba yawa gaske angama rabawa mutanan balaja'u da yan ƙwalta me zanyi da ragowar ƙadangarun bariki, yana gama faɗar haka ya bar gun jikin tane ya fara rawa ganin ya zame mata yawa mayinwacin zaki ganin ba zata iya mayar mai ba bata taɓa zaton akwai mutumin da zata ji tsoro ba bata san irin tsanar da tayi mai dare yayi bata da niyar barin ɗakin yasa ya ɗauki pillow da blanket yace "Ungu ki haukan waccan kujerar ki kwanta yanuna mata wata kujera me kama da gado , Jikin ta a sanyaye ta amsa ta hau tayi addu'a shi kuwa kitchen ya je ya ɗauko system ɗinsa ya fara duba wasu file da muzamfar ya turomai abubuwa sun mai yawa gashi zaɓe ya kusa ga kasuwanci sa gobe ma zai tafi Saudiyya sai ana jibi zaɓe zai dawo duk wani abu ya tattara shi ya adana dan ma ya gamu da ɗan uwa na gari ba abin da zai cewa muzamfar sai godiya tana kallonsa domin inta rufe idonta mucijin nan take gani pajamas yasa farare ta da su ya ɗauro alwala system ɗinsa ya ɗauke ya ajjiye ta haka files ɗin ya mayar dasu cikin briefcase ɗinsa gobe zai bawa muzamfar yasa hannu a taƙardon daman cewar shi ake jira shin fiɗa daduma ya tada kabbara bayan ya idar ya ɗauki Alkur'ani ya fara rera ƙira'a ne daɗi yawa Balarabe Sa'udiyya ne keyi nutsuwa ce ta shigeta ta lumshe idonta amma ba bacci take jiba ganin ya kashe lamp ne ya kunna dum light addu'a yayi ya kwanta kasa bacci tayi sai juyi take ganin ya daɗe da bacci yasa ta tashi ta fara sanɗa a hankali ta hau kan gadon wani irin tsoro take ji ga wasu mutane da take gani kamar a mafarki yaji annanuƙeshi tashi yayi ya ƙalleta yace "Ina ance miki yar iska kice ke ba ita bace inban da jaraba irin taki rana ɗaya baki baki kwanta da namiji ba shine duk kika fita hayyacinki to ni wallahi nafi ƙarfinki na adana kaina na kamilar mace ne wacce bata rabawa yan iska kanta ba to maza sauka ko in fasa miki jiki ni ba haka nake ba yarinya ƙarama dake sai son maza, Jikin ta a sanyaye gwaninɓan tausayi ta sauka ƙasa nan yaga jini har jikin sa yace "Ke ƙazama zo wallahi yau ba sai gobe ba zaki ƙwanke min kayana ke wacce irin ƙazamace yau zanyi fornitionment ɗinki yarda gobe ko ance kiyi ba zaki ba sannan harda na ƙwanta min a gadona, Ƙasa tayi da kanta kunya duk ta ishe ta koma me ai ita ta jawa ƙanta tashi yayi ya fita sai gashi ya dawo da jimgegen blanket dinnan ga kuma na yanzu da ta ɓata da jini cire rigar sa yayi yace "Maza ɗauki ki wanke min su tas, Ɗauka tayi ta shiga toilet ta fara wanki iya huya ta cita ba ƙarya ƙugunta yawa ya ƙarye bata gama wankin nan ba sai 03:00 daidai yana zaune a kan kujera yana kallon ta hannusa ruƙe da bulala fitowa tayi yace "Ai ba kwanciya zaki ba ga rigarki ɗauki kisa ki ciremin tawa ki wanke, Dubansa tayi da rinannun idanuwanta sunci kuka sun gaji tace "Wallahi na gaji, Yowa ƙanta yayi da gudu ta ɗauka ta wanke ta tas ta sa tata yace "Good girl sauran wankin mota domin gobe zanyi tafiya, Ɗurƙusawa tayi tace "Wallahi ban iya ba , Tashi yayi ya ɗauki key din motarsa yace "Zama ki iya ne taso mutafi ai ba guda ɗaya zaki wanke ba suna da yawa, Ba yarda in kinsiyi littafina ki fitar min da shi ku tausaya min typing akwai huya kiji tsoron Allah yar uwata ƙarki fitar min da littafi na Yarfa hannuwanta tayi tace "Ni wallahi ba inda zani baka da tausayi ne ?, Wani bazan kallo yayi mata yace "Mutanan da suka san darajar ƙansu su ake tausaya wa ba ke wacce daraja ce da ke kin gaba nuna pictures ɗinki a social media kin gama rawa , Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tare mata ma ƙogaro tace "Wallahi duk abin da kake faɗamin sai Allah yayi min hisabi da kai ba ko wacce yar social media bace yar iska ko wacce da irin nata halin, Banza yayi mata ya tisa ta gaba sai tayi wankin mota faƙar idonsa tayi ta waɗa toilet ta rufe bugun duniya yayi taƙi buɗewa Yace "Wallahi sai de in bazaki fito ba mu haɗu gobe, Tace "Ehɗin naji mugu kawe Ganin dare yayi bata da niyar fitowa ala dole ya nemi gu ya ƙwanta cikin sanɗa ta leƙo ƙanta ganin yana bacci a hankali ta fara tafiya jitayi an fusgota ba zato ba tsammani ta jita kane kane ajikinsa sakar mara nauyin sa yayi yace "Kina zaton zanyi bacci ne yarinya duk kan wani motsinki a tafin hannuna kike , Ture shi ta shiga yi ganin ko matsi ya kasa yi cikin wahala ta zaki kuka tace "Allah sai ya saka min kana cutar dani ka ɗagani ni ba yar iska bace, Dariya saki ya ɗora ƙansa a ƙirjinta yace "Au Allah ni kuma Ni ne ke zuwa club har ake faɗa dani a tiktok ko, Toreshi tayi tace ''waya sani abu a duhu, Ɗaga ta yayi ya tashi ya canza gu ya kwanta yayi addu'a ganin ya fara bacci itama ta ja blanket ta ƙwanta ni kuwa nace asuba ta gari Wannan kenan Duk irin duhun dajin be da mesu ba ga wani irin kukan tsintsaye ɗaƙar suke iya tafiya saboda wani irin tsauni haka suka nufa wata bukka wani irin ihu suka ji aka ce musu ku tawo da baya la'anannu aikuwa suka juya bayan su suka shiga wani irin ƙatotan mutumine gashin sa duk a cuƙurƙuɗe wajan sai ƙarnin jini yake ga wani irin wari ƙasu suwan mutane ne kala kala a zube buɗe bakinsa yayi wani irin wari ya bugesu nayi mamaki me wayan nan yan gayun mutanan keyi ba ɗigon wahala a tare da su baƙinsa wani irin ruwane ya fito me yauƙi yace "Hhhhhhhhh ai daman nace muku zaku dawo duk wajan wanda zaku je magana ɗaya ce dole sai yayi bani da damar taɓashi kullum yana tare da alwala ga addu'ar da mahaifiyarsa ke yi masa na tura mishi ɗantsandu a subfar mucijii amma ya dawo a ƙone hhhhhhh, Ɗayan ne ya gyara zama yace "Yanzu boka dole ne sai yayi mulki baza a iya kashe shi ba?, Hhhhhh babu dama amma zamu hanashi cin mulki lafiya za'a zubar da jinin mutane hamsin sannan za'a cirewa yara yan shekara goma mata idanu sai ayi amfani dasu kai ne kuma za kai Yanuna wani attajirin mutun naso in sheda fusƙarsa amma narasa inda na san shi Zaro ido yayi yace "Ranka ya daɗe ko za'a canza min aiki ne , Ɗayan ne ya ɗanne mai ƙafa alamun yayi shiru Boka yace "Dole kai za kai kana gamawa ka cire musu ido , To amma bazai yiwu a dadashe taurarinsa Boka yace "Ba zai yiwu ba taurarinsa suna da ƙarfi ko munyi yin ƙurin ta ɓasu asirin ka ne zai tonu, Toto abarshi tashi sukai da baya da baya suka fita Oni oum Yasmeen KO su wane wa yannan 🤔 Wannan kenan LIMON FEDERAL HOUSE Faɗar shugaban ƙasa Kaiwa yake yana komowa ya rasa me ke mai daɗi yaso yayi shekara taƙwas amma ba dama alamu sun nuna bashi talakawa ke soba irin wannan ɗaular baya fatan barinta duk sanda ya fita yaga talakawa a ƙasan sa suke shi ke jin ragamar rayuwar su in yaso ya barsu su wahala in ya gadama ƙaisa ƙara girma yake yaga shi ke juya su ga uwar jiniyar da ake mai ba yashi kowa a ƙasan sa yake giyar mulki na kansa President bamu da wata mafita dole kabi maganar boka kasan in muku haɗashi faɗa da talakawa mun haɗashi da babban aiki zamu sa ana kashe kashe kaga ace shi keyi musa sojojin baka su addabe shi duk da da wacce muka ɗogara tayi ɓatan dabo a ce saboda ta faɗi gaskiya ya sa asace ta tunda bayanai sun nuna batanan koma ta mutu kaga a gaban kowa akai haka office chair ya ja zauna yace "Na bar maka komai a hannuka yau in dare yayi aje ƙauyan ciranci a kashe mutane hamsin a tawo da yara goma wa yanda ba zasu huce shekara goma ba su, Ko kai fa shekara huɗu kamar yace kaga kuma daman yanzu a gangar siyasa ake sai kaje ka kai musu jaje harda kukan ka ka basu tsaba tunda su kajine kana watsa musu zaka ga sun fara tsassaga Wata dariya suka sheƙe da ita duk kansu yawa wasu arna Allah kasa mu dace siyasa mugun wasa Allah kasa muyi kyakkyawan ƙarshe Barka da da Sallah Cikin mayan ƙaya ya shirya tsab yace "Yau mubaraka zata zo ta kawo miki kaya Ni zan tafi Saudiyya , Da sauri ta ɗago ta dube shi tace "To yanzu ba zaka duba Allah da Manzonsa ba ka bani jakata ba, Akwatin sa ya tsayar yace "Bazan bayar ba , Kwanciya tayi a saman kujera tace "Allah ya tsare , Juyowa yayi be taɓa tsammanin faɗar haka da gare ta ba yau ne karon farko da ta bashi tausayi yace "Ameen ya fita , Ganin ba sarki sai Allah ba shirita tashi ta nufi kitchen domin ɗora ɗan wani abinci ruwan indomie ta ɗora ta ɗako guda ɗaya ta fara dafawa ta ji kayan lambu ƙashe gas din tayi ta juye a faranti ta fito jin sallama tayi amsawa tayi ganin matashiyar budurwa ba zata huce shekara ashirin da daya ba hannuta ruƙe da yarinya ƙarama yar kimanin shekara 4 tace baby gwon pink colour an mata two baby da kanta fara'ar fusƙarta ta faɗa ɗa tace "Sannun ku da zuwa, Mubaraka tace "Yauwa anty zarah mun same ku lafiya , Jin sunan da ta kirata da shi yayi mata ban baraƙwai miƙawa mufeeda hannu tayi ai kuwa tazo gunta tace "Anty ina kwana, Yarinyar ce ta shiga ranta tace "Lafiya qalau babyn, La uncle ya faɗa miki sunan da yake cemin Ɗauƙan ta tayi tace "Uhmmm , Zama sukai kitchen ta shiga ta buɗa fridge ta ɗauko lemo me sayi da fruit salad ɗauke try ta jerasu glass cup ta ɗauko gudu biyu a kitchen cabinet mufeeda sai surutu take zuba mata ita kuma tana biye mata a Centre table ta ajiye mata tace "Bisimilah , Murmushi mubaraka tayi tace "Sannu da aiki, Yauwa tace ta koma gefe tayi ƙasa da ƙanta wani sojane ya shigo da kaya nuƙi nuƙi bayan ya gama shigowa da shi ya fita mubaraka tace "Duba in da akwai abin da be miki ba ki faɗamin gashi nayi ƙunɗun bala na nazaɓar miki undis sai ki gwada na tambaye shi yayi min shiru, Dubanta tayi tace "To Nagode, Mijin ki zaki wa godiya ni nawa zaɓane ƙinsan ɗan kasuwa ne to a store ɗinsa yace inje in zaɓar miki Ɗaga ƙanta kawe tayi floor ya ɗau shiru bakajin ƙarar komai sai ta ac sai surutun mufeedah tashi tayi ta shiga kitchen ta ɗauko indomie ɗinta suka ci tare da mufeeda bayan sun gamaci ta wanke mata hannu tayi bacci bedroom ɗinta ta ƙaita ta ƙwanta ta fito ta zauna a floor sosai mubaraka ta shagala da charting ɗinta ganin anty zarah ba me son magana bace ganin ta yi shiru mubaraka tace "Ƙunyi waya da ya azzam ya sauka?, Ƙasa tayi da ƙanta tace "Bani da waya, Okay bara in kira miki shi Dan Allah ki bari kawe Okay nabari yawa wanda ba auran soyayya kukai ba Shiru Binta tayi mata To Ni zanta fi Wani murmushin manufa tayi tace "To Bara in ɗauko miki baby ko, Eh , Tafiya tayi ta ɗauko ta tace "Bara in raka ki , Aa basai ƙin rakani ba Wallahi sai na raka ki muje fitowa sukai sai yanzu ta ware idonta tana ganin komai wani sojane ya taso yace "Oga yace ƙar mu barki ki fita indai ba da sanin sa ba ki koma ciki , Duban sa mubaraka tayi tace Rakoni tayi Wani banzan ƙallo yayi mata yace "Wannan ba umarnina bane na ogane dan haka ki koma ke kuma zo ki tafi ƙin huce ƙa'idar lokacin da na baki , Ganin bashi da mutunci yasa tace "Anty zara sai wataran, Ƙai Binta ta daga mata yawa ƙadangaruwa faƙar idonsa tayi ta fita a guje tuni suka bita ɗayan ya tsaya yace duk wani gate na gidan a rufe da yake gate huɗu ne ta huce na farko amma tana zuwa na biyu ta ganshi a garƙame ga wasu irin murɗadɗun sojoji sun saita ta ta da bindiga saranda tayi ogansu ne ya zo yace "Maza zo ki koma , Tafiya ta fara tana waiwaye tana zuwa taga ya buɗe mata wani ɓangare me ƙama da ƙurkuku yace "Shiga nan , Ba musu ta shiga ɓanɗaki ne a ciki sai tabarma ta kwanciya sai kayanta da mubaraka ta kawo mata zama tayi ya kulle ɗakin yace zan din ga torowa ana baki abinci ya bar gun Wani irin baƙin ciki take ciki ga wata ran ma in aka Kawo Mata abinci bata ci sai dai su zo su ɗauka a haka har ta ɗau satibiyu a gun fatar tata tayi wani irin kyau da goge bata shiga rana a haka har aka kaɗa gangar siyasa Ana sauran ƙwana biyu zaɓe azzam ya dawo sai dai a kura ya sauka gun kakansa shi ya manta da rayuwar wata Binta sabgar shi yake sosai a ka shiga harƙar zaɓe gadan gadan yau akai zaɓe gwamnoni inda isa birnin malin yace ɗan jam'iyyar su azzam sosai al'ummar gari suka cika da murna sai bayan sati ɗaya za ai na shugaban kasa addu'a Alhaji Ibrahim Bashir kura yasa ayi da masu sauƙar Alkur'ani gari ya rukice jira ake aga wanda zai ci ɓangaran Binta kuwa bata san me akeyi ba tun da har yau tana ɗakin nan a tsare Wannan kenan Muzamfar yace "Azzam Ni kuwa ina Binta , Shiru yayi na wasu a wanni yace "Tana gida mana , Amma kazo ka tare a nan ba ka gudun kaɗaici yayi mata yawa ta sami matsala ne Banza yayi mai ya fita Rana bata ƙarya An zuma tsaro a kasar duk inda kaje jama'a ne ciki ana gudanar da zaɓe duk da wasu ƙananan hukumomin an sami matsala anyi faɗan daba fito yayi zai je inda yake da aƙwatin zaɓe shi shida muzamfar mota biyu ce ta raka shi ya ɗan gwala yatsan sa ya ɗaga tuni yan jarida suka shiga haskawa kai tsaye bayan ya gama ya shiga Mota ya koma kura Ita kuwa binta bata da lafiya sosai jikin ta yayi wani irin zafi ta rame sosai ganin ogan su bashi da lokacin amsa waya basu yi wani yin ƙurin kiran sa ba sai panadol da suka siyo mata aka ajiye mat a bata shaba domin a halin yanzu bata da ƙarfin cin wani abu komai taci sai tayi amansa Ƙarfe 4:30 ɗakin fardar sakamaƙon zaɓe shigaban jam'iyu sun taro sun taro da jama'ar gari tuni Farfesa Sadik Sani ya sharce gumi ya tuni shugaban nin irka a ƙwati sun gama aikin su an miƙo mai duba wa yayi ya fara jero yan taƙarkaru jikin kowa yayi sanyi da ƙƴar ya buɗe baki yace "Mu'azzam Bilal Ibrahim kura shi ne ya lashe zaben shugaban kasa , Tuni gun ya ɗau kabbara Sannan yace "Masu ganin ba ai musu a dalci ba zasu iya ƙai kara kutu nan da sati ɗaya , Tashi yayi aka raka shi filin jirgi Wannan kenan Yana ji ya ɗur ƙusa yayi wa Allah godiya Hajiya Turai ma haka tace "A yau Allah ya dora maka nauyin al'umma sai ka ɗaure kai a dalci , Insha Allah yace yan uwa da aboka nan arziki suna ta zuwa ta yashi murna a yau zai shiga fadar shugaban ƙasa tuni yan uwa na kusan sa da aboka nan siyasar sa suka yi mai rakiya har da Alhaji Ibrahim ancan za ka mai na gidan addu'a yayi ya shiga da ƙafar dama anci ansha anyi hoton tarihi kowa ya watsai Sai ƙarfe shaɗa ya sami damar shigowa gida kallon komai yake yawa a mafarki ban garansa da aka ware mai ya nufa kai tsaye bedroom ya shiga yayi wanka ya ɗauro alwala ya shimfida daduma ya fara lafilah bayan ya idar yayi karatun Alkur'ani kamar yarda ya saba sannan yayi shirin kwanciya yau kawe sai yayi sha'awar buɗe jaƙar Binta da yake tun jiya muzamfar ya kwaso mai kayansa wata loka ya buɗe ya ɗauko zip ɗin ya buɗe nan wata farar ta ƙarda ta waɗo ba wani tar kace a cikin jaƙar wayar ta ce sai ATM ɗin ta sai lipstick sai turare da taƙarɗar nan wayar ya ƙunna pic ɗinta ne a screen ɗin wayar tayi kyau ɗannawa yayi yaga ba security gallery ya shiga pictures ɗin tane sunfi dubu ita da kawayanta haka kurum ya shagala da kallon su wasu yayi murmushi wa yanda take tare da maza ya goge ya dade a haka ƙarar shigowar message a wayar sane ya ɗauki hankalinsa fa sauri ya duba inda ya zaro ido ganin me aka ce a text ɗin number yabi cikin bada umarni yace "Ku kawo ta nan , Be jira me zai ce ba ya kashe takardar ya kasa budewa ya mayar da komai ya zuge ba a jimaba sai sukai mai waya ga sunan fitowa yayi har wajan motar ya nufa ya buɗe kallon yau she gamu yake mata duk ta rame ƙasa yayi da murya yarda ita kadai zata jishi yace "Sannu ya jikin naki, Harara ta watsai mai yawa idonta zai faɗo ƙasa ta murguɗa baki a fakai ce take kallon sa yawa an ƙara masa kyau kyan jikin sa yana ɓoye shekarunsa ya ƙara zama babban mutum ni kuwa nace yanzu fa binta shugaban ƙasa ne fa Murmushi yayi yace "Uhmmm kalleni da kyau me ya faru zahra daga sannu sai harara ?, Haɗe rai tayi ta kauda kanta tace "Me zan kallah ni ba kallon ka nake ba matsamin in huce , Yace "Daga baya kenan, Matsa mata yayi tare suka jira duk abin nan da take ƙarfin haline bata da wata ishashshin ƙarfin jiki hannu ta ya ruƙe ƙoƙarin ƙwace wa take amma yaƙi bata dama ta jinjina ƙarfin mulki irin tsarin da a kaiwa gidan yayi kyau bataɓa mafarƙin shiga wannan ɗaular ba yau gata a limon kuma a gidan shugaban kasa baki da hanci ta saka tana kalle kalle ga wani irin shegen tsaru da aka bawa gidan hannunta ya matsa yace "Yar ƙauye , Yar ƙara ta saki tace "Wallahi bana son mugunta, Wani musƙilin murmushi yayi me cike da ma'anoni kala kala yace "Ga shi na iya ta ko to wallahi ki guji ranar haɗuwar bakiji dadi ba duk maganganun da kike faɗamin sai na fanshe su tasss, Banza tayi mai ta shiga wani tamfatsatsan floor na alfarma tun daga ƙan curtains ɗin har luxury furniture ɗin blue ne da a don golfing colour iya kyau da tsaruwa sunyi ga wani irin carpet kana taƙawa ƙafuwanka na nutsaiwa saboda taushi Azzam yace "We ke me isa a rayuwar ki kin iya kauyan ci sai a sami gu a zauna ko ko baki gama kauyan cin ba ?, Shiru taimai domin yanzu magana bata dameta ba abubu sun mata yawa yan zu tasan ko giyar wake ta sha baza ta iya fita daga gidan shugaban kasa jikin ta a saliɓe ta zauna yawa an wanke kaza da ruwan sanyi mayafin ta gyara ganin irin kallon ƙurirlar da yake mata ciki ciki tace "Mutum sai shegen kallo in magana ace ni nake yii, Ɗora kafa ɗaya ƙan ɗaya yayi yace "hmmm ai ba sharri nayi miki ba na sha kamaki kina satar kallo na kinga handsome boy mijin mace hudu, Zaro ido tayi batayi zatan zai jita ba ta murguɗa mai baki tace "Kayi abin da ya fi hudu ko ajikina sai ka sallameni , Uhmm yawa gaske sai anyi ido ya raina fata ai wallahi ni da ke mutu karaba in zaki haƙurama da ya fi miki alkhairi alƙawarin nayiwa kahunki ni bana saɓa alƙawari Kallon sa tayi cikin ta'ajibi tace "Mu zuba muga ni (next book ɗin na kenan duk wanda ya siye binta yar jagaliya da farko kyauta zan bashi MU ZUBA MU GANI ba sai ya siyasa ) Kallon ta yayi ya jinjina kai alamun zan kamaki ne yace "Yanzu Dr zai zo sai ki shirya , Ƙasa tayi da idanunta ganin irin wani mayatatcan kallon da yake jifanta da shi ji tayi duk ta ta kura tace "Ni wallahi naji sauƙi , Mu'azzam yace "Naga a lama yar jagaliya ko baka ake ce miki ?, Ƙanta ta ƙwantar a hannu kujera ta lumshe ido Wayar shice tayi ƙara ya ɗauka yace "Okay Ku barshi ya shigo, Ya kashe yace mata ga Dr nusaiba nan shigowa sauran ki wani abun da badai dai ba wallahi bayan ta fita in huƙunta ki Haɗe ranta tayi ta cuno baki tace "Uhmmm, Yace "Wallahi ki ci gaba da turomi baƙin ki wataran zan hukunta ki ne ko cewa akai kimin ba zaki ba ƙaraba, Duban sa tayi ganin ya ɗaga mata gira ta ɗauke ƙanta gani take yawa ba shiba karmar canza mata shi ƙamar ba wanna mutumin ba da magana ma huya take mai sallama Dr nusaiba tayi amsawa sukai cikin girmamawa ta gaishe su duban Binta tayi tace "Kece mara lafiyar?, Kai ta ɗaga mata Dubata ta farayi tana tambayar ta tana bata amsa ganin cutarta ta damuwace ta assasamata ta dube shi tace "ba abin da ke damun ta sai dai in ta cigaba da sa ƙanta damuwa zata kamu da ciwon zuciya yanzu zan mata allura naji jikin ta da zafi sannan zan rubuta magani da allurai har na kwana ukku, Zaro ido tayi ta matsa daga inda take ta marairaice murya yawa zatai kuka idanuwanta sun ciƙo da ƙwalla cikin salon shagwaɓa wanda ita bata san tayi ba tace "Dan Allah Dr ki rufan asiri wallahi bana son allura bana son magani ba kin ban shawara ba zan kiyaye, Allah ya sani in tayi shagwaɓar nan susuta shi take yana rasa nutsuwar shi notin ƙansa ya ƙunce ita kuma ya lura ɗabi'arta ce nutsuwa ya aro baby face ɗin ta ya kalla yace "Ke nan a ƙƴale ki da ciwo ko, Ai ta ban shawara Uhmmm hakane yanzu a kwai a gunki "Eh bara in fita in ɗauko ta ajiye mai taƙardar da tayi rubutu ta fita bata daɗe ba ta dawo kallon ma'auratan suna bata sha'awa komai na azzam burgeta yake Allah ne ya nufa ba zai aure ta ba ƙwallah ta share ta fara haɗa allurar cike da sha'awa take kallon ta tace "Na gama zo in miki bani da zafin allura, Tashi tayi zata gudu ya ɗan ƙota yace 'a ina za'a yi mata?, Dr nusaiba ta zauna a kusa da Binta tace "A hannunta, Zip din rigar ta ya zoge ya zaro hannuta wani irin laushe da santsi mafatar yaji tana yi ya ɗanne ta yace "Yi mata, Tayi ƙoƙarin kwace wa amma ko motsi bata yi ma har a ka gaba kukan shagwaɓa ta saki domin har ga Allah allurar ba zafi itama kawe ta sinci ƙanta ne tana kuka Dr nusaiba tace "Allah ya tashe mu lafiya ke kuma uwar raki zaki gane allura ba wata ba bace lokacin da kika zo haihuwa , Cak ta dena kukan ta ɗago ta kalle ta Nusaiba tace "Kalle Ni kyau a zafin allura ko ƙwatan haihuwa be kai ba, Mai da kanta tayi ta kwanta a cinyar shi tana mai da a jiyar zuciya Tafiya tayi kogin tunani ya shiga tambas maganar da Dr tayi ta tunasar da shi son ƴa'ya inama yana da su kallo ta yayi ko zata iya yar da ta haifa mai baby ne ko da gaske take da take cewa ta tsane shi ganin bashi da amsar tambayar sa ala dole ya ƙauda tunanin yace "Kinji ƙunya babba dake kina kukan allura ai wannan ƴa'ƴan mu zaki barwa , Tashi tayi daga kwanciyar da tayi tace "Ƴa'ƴa kuma kai dawa?, Waskewa yayi yace "Babyn nake nufi, Ni kuwa tana ina yarinyar na da surutu Yace "Kamar ke, Binta tace "Ae ƙƴan ƴa' ta gaji iyayenta, Mu'azzam ya dubeta yace "Gyara hannu ki ina ganin komai fa ko da yake ai sadakina na kallah ba haramba, Sauri tayi ta kalli ƙirjinta saman maman ta ya fito da sauri ta zoge zip ɗinta suna haɗa ido ta galla mai harara Yace Yarinyar nan na lura raini ya shiga tsakanin mu ko zan maganin ki Toro baki tayi bata ankara ba taji bakinsa kane kane cikin nata wani irin kiss yake mata ga kamshin mouse mint din da yayi amfani ya haɗu na ta meƙamshin 🍓 bakinta yana bada wani kalar ƙamshi ƙoƙari take ƙwace amma ina ta kasa kuka ta shiga yi badan ya gaji ba ya sake ta a'a sai dan kukan da take tasss ta shanye yahunsa amai ta shiga ƙakari amai ba abin da ya fito Dariya yayi yace "Gobe ki kuma kiga yar da zamu ƙwashe , Banza tayi mai bakinta duk wani irin radadi yake ga yar ƙumburar da yayi Yace "Kinji dai abin da tace ki daina damun kaiki mene matsalar kine, Tashi tayi ta barshi a zaune domin wannan tambayar rainin hankali ce cak ta tsaya saboda bata san ina zata nufa ba ta juyo tace "Inane bedroom ɗina ?, Dariya yayi yace "A ɗakina mana , Zaro ido tayi tace "Allah ya sauwaƙe nii, Ɗaga mata gira yayi ya kanne ido yace "Ƙaryar banza kina murna saboda an daɗe ba a haɗuba, Kuka tasa ta fara tafiya jitayi cak ya ɗauke ta wutsul wutsul ta shiga yi mai be dure ta a ko ina ba sai ɗakin sa ...... Tashi tayi zata fita ya ɗanna remote ya kulle kofar a aljihun wandonsa ya sa ya kalle yace "Ko zaki ɗauko ne?, Jingina tayi da jikin ƙofar tace "Aini ba yar iska bace, Har zai shiga toilet ya tsaya yace "To wane dan iska ?, Hannu ta wara mai a lamar oho Gir giza kansa yayi ya shiga toilet aljannar duniya kamar ka zauna kaci abinci kwankan tsarki yayi ya sanya jallabi maron colour ta mashe shi sai kamshin turarukan wanka yake alwala ya sake ya fito tana inda take nunawa yayi kamar be ganta ba kashe fitila yayi ya zare rigarsa daman baya kwanciya da kaya a jikin sa inde ba sanyi ake ba daga shi sai bosser ko dum light be kunna ba yayi addu'a ya kwanta yaja duvet ya lilluɓa Ja da baya ta ƙara ganin irin halittar sa jikin ta ya ɗauki rawa gumine ya shiga yanko mata ganin kamar yayi bacci saɗab saɗab ta shiga toilet cire rigar ta tayi ta fara wanka hankali kwance ta manta bata kulle kofar ba saboda ta saki fanfon bathtub bata san da mutum ba ji tayi an taɓata gigice wa tayi ta saki wata ƙara ta miƙe 4eyes sukai da shi saurin ɗurƙusawa tayi Allah ya rufa mata asiri kumfa ta cika ƙurmin wankan rufe idonta tayi gam tace "Wannan wanne irin hulaƙanci ne tsakani da Allah ai kasan ina toilet ɗin nan tun da zaka ji zubar ruwa shine ka shigo halayen ka ne yasa nake maka wani abun wallahi, A zuciyarsa yace lallai yarinyar nan in be fitar da rauni a tsakanin suba baza ta nutsuba Kamar an dasa shi haka ya tsaya a jiyar zuciya yayi ya shiga cikin ƙurmin ƙara ta zunduma zata fita ya ruƙota wani irin toreshi take amma ina ƙarfin mace da namiji ba ɗaya ba kuka ta shiga rai rawa ganin ya fita hayyacinsa duk irin magiyar da take a mai be saurare ta ba so yake ya rabata da abin da tayi shekara da shekaru tana tattalinsa tayi faɗa akan sa saboda maza da yawa sun kawo mai farmaƙi ta hana kanta jin dadi duk dan mijin da zata aura ya ganta da daraja yau gashi wani a ɓagas zai sameshi akan sadaki dubu shidda kuma an mata aure ba sanin ta an sato ta tana cikin jin dadin rayuwa cizo ta gasa mai a dantsan hannusa ko a jikin sa saima daukan ta da yayi ya fita da ita be dureta a ko ina ba sai a gado addu'ar saduwa da iyali ya shiga karantowa kamar haka بِسْمِ اللهِ اللّهُمَّ جَنِّبْنَا الشَّيْطَانَ، وَجَنِّبِ الشَّيْطَانَ مَا رَزَقْتَنَا. Taje islamiyya duk da bata yi wani nisa a karatu ba amma ta san wannan addu'ar me ta ke nufi hankalin ta ne ya ƙara tashi ta saduda domin yanzu bata da wani ishashshan ƙarfi ta gaji da ture shi da take ashe ma kuka samin dama ce ita yanzu ba hawaye sai na zuci ji take ƙirjinta na wani irin ciwo saboda abun da yake musu tunda take ba mahaluƙin da ya taɓa kai hannu inda ya kai yanzu ɗauki take nema amma da alama ba me jinta ganin lamarin nashi yayi yawa wata irin duniya yau zarah ta kai shi tunda yake be taɓa suntar ƙansa a cikin ta ba ya godewa Allah sai albarka yake sanya mata tambas samin irin zararshi sai antona suna huya a cikin mata ba ko wacce mace bace ke da irin baiwar ta ba ba shiri na fita ina sa ƙafa a floor naji wani irin ihu me haɗe da kara Na sheda yau ya mai da ita ci kakkiyar mace nikuwa nace asuba ta gari Wannan kenan Allah Allah su Ramlah suke gobe tayi domin Hajiya Turai tace zasu je gidan azzam daga nan zata barsu suyi wata ɗaya ita kuwa yusrah haɗa baki sukai da mahaifiyar ta zata takurawa zarah ta hana ta saƙat harta hassasa zargi a tsakanin su domin zata je gidan ne da mafofi harda maganar boka da ya tambatar musu cewa bazai taɓa kusantar taba zai jima baya son ganinta a kafin ai zaɓe taga kamar maganin yayi aiki domin ta sami labari tunda ya dawo be je gunta ba haka har yaci zaɓe be waiwayeta ba gashi ya shiga gidan shi ƙade sai da ka baya zata zo ko iya wannan suka sami nasara ai sun dace Sha'awara matan kuji tsoron Allah ku dena kai maza gun bokaye har ku kauce hannya kunsan Allah ba zai bar ku ba kuma wannan shirkace Allah kasa mu dace Masu iya magana sunce waiwaye adon ta fita Tunda ya dawo daga umara komai nasa ya canza magana kaɗan sai ansa kalmar Larabci haka uwani ta dena siyar da kamai yanzu yana iya cida su dashi sai uwani meragaji ta yi aure haka saminu kuwa yana ɗan buga bugarsa lawandi kuturu wallahi wannan yaron namatasa surikina ne Raƙen da yake sha ya daka ta da sha yace "Eh ba shakka nace ba shakka labahani yanzu ƙaryar azzuƙin naka har ta kai haka ?, Duban sa yayi ya ƙar kata hula ya washe baki ala dole sai anga haƙurin Makkah da ya sa har guda shidda abikin sa fari da Golding yawa ni ɗan ɗaudo saminu yayi yayi dashi ya cire yaƙi yace sai de in ya mutu a cire a binne shi amma bashi ba cirewa yana yimai baƙin ciki ne yace "Yasin ba ƙarya nake maka ba lokaci yana nan zuwa nima zan tafi limon inje inga ɗiyata ko yanzu ta haihu , Ta kaicine ya addabi lawandi kuturu Ya tashi ya ce "Na tafi , Zazzaƙallahu ƙhairan ya aƙi Harara ya ɗan karamai yace "Inma zagina kake kaje kai da Allah Hhhhhhh godiya fa nayi maka saboda ziyarar da kai min Kaji dashi dai ya tafi Wannan kenan Bayan Binta ta gudu nan aka sami wanda suka tausaya wa mahaifiyar rufaida suka sake ta ba irin tsinuwar da bata yiwa binta ba ita kuwa rufaida da ƙƴar suka rabu da zanburuta cewa sukai ai su sukai wahala ba ita ba bayar da ta iya haka ta ƙarbi dubu ɗari huɗu ta tafi Lagos agege ta kama ɗaki ta zama uwar karuwai sosai take jin dadin duniya ta manta da rayuwar Binta ba irin magiyar da mahaifiyar ta da Bata yi mata ba amma ta mussuƙe ido tace mata anne mi Binta an rasa amma ko a jikin ta cewa tayi Allah isa ta mutu Har mahaifiyar ta ta cika bata zoo ba cewa tayi Allah ya jiƙan musulmi Hausawa sunce in zaka gina ramin mugunta gina shi ƙaɗan ayau ta tashi da wata iriyar cuta tun da taje gidan yin blue Film 📽️🎥 ta dawo ba lafiya ta yau kuwa tafi ta ko da yaushe ko ɗaga hannuta bata yi tana cikin wannan hali taji an bugo mata kofa ko tasha bazata iya ba wa zata gani ministan da ta haɗu dashi wancan satin hujiga hujiga da ƙatuwar huƙa yace ''kin cuceni ashe kina da ƙanjamau baki faɗan ba yau naje aka dubani likitoci suka tabbatar min kuma kece mace ta ƙarshe da nayi ma'amala da ita , Zaro ido tayi tana kwance tace "Wallahi ban sani ba samila kin cuce ita ta rakani gidan yin blue Film wayyo Allah na bani da gata ba uwa ba uba Ni kaɗe iyayena suka haifa dan Allah ka tausaya min , Marinta yayi yace ''kina da hankali kuwa lallai yau zan miki rashin mutunc... tana kuka tana komai ya cireka mata nono ɗaya yace Wannan ita ce irin saƙayyar maciyin amanah ya fita Ba wanda zai temaka mata suma kansu yaranta yanzu sun dena jin maganar ta a cikin suma masu yin less tana zaune zasu yi wani ma harya ce zai rage zafi da ita duk kuwa da irin halin da take ciki ta zama kamar wata mahaukaciya cewa take kukai gun binta da ƙabarin mahaifiyata in nemi a fuwarsu nasan hakkin mahaifiyata ne da na Binta ke bina haka zasu yi ta dariya suna shewa ƙarshema sai suka fitar da ita waje suka watso mata kayanta ko bara bata iya yi gaban ta na wata iriyar tsotsa yake da wari Shawara Ƙar ki yarda kibi ruɗin duniya kuɗi mulki me ƙarewa ne ke nemi rufi asiri kada ki biyewa ƙƴaleƙƴalan duniya yana da iyaka ki nemi amincewar Ubangiji duk abin da ya dameki ki tashi cikin dare ki faɗawa Ubangiji a lokacin addu'ar bawa da Ubangijin sa ba hijabi wannan kenan A gigice ya tashi ya nufi fridge ya ɗauko ruwa me sanyi ya buɗe bakin gorar ya sheƙa mata ihu tayi ajiyar zuciya ya saki ya ruƙe ta kuka take tana ture shi haƙurin duniyar nan ya bata taƙi yin shiru ga farin zanin gadon yawa anyi ɓari jini kai kace sa aka yanka sosai ya ruƙice da ganin jin nan Dr nusaiba ya yiwa text message ya koma ya ɗauke ta ya shiga toilet da ita sau uku yana sata a ruwan zafi tana wani irin kuka tana ƙoƙarin tashi yace "Ai zaki iya wanƙan sarki ko, Kai ta ɗaga mai bakinta ya mutu bata iya magana komai ta ciwo yake mata fita yayi ya shirya domin yau yana da taro da gwamnoni nadan ransa ya so ba zai barta a halin da take ciki yaso yarda ta bashi farin ciki yau ya huni da ita ya dasa mata soyayyar sa a zuciyarta yau ya tambatar dace wa Binta kamilar mace ce ita yake mafarkin samu sai gashi Allah ya bashi wata irin ƙimarta yake gani Shawara Mata duk runtsi kar ku bari ko je gidan mijin ku ba buɗurcin ki Kar Ku biyewa kururuwar sheɗan ya ingiza ku ku waɗa halaka ƙar ki yarda saurayi yace auranki zai yi ki bashi wallahi zaki yi dana sani mara iyaka kee za'a gani a jikin ki shi kuwa ko kullum zai yi ba me ganewa kuma har abada tabonnan ba zai goge ba a idon mijin ki da jama'a zace ai ya'yan wacce ta taɓa yawon banza ce abin ya dinga binki kenan babban floor suka haɗu da musiba tace "Good morning president , Morning kawe yace yayi gaba security rintin sa na jiran sa kar ɓar briefcase 💼 ɗinsa yayi suka fita duk inda ya taka girmama shi ake ana sara mai ake me aikin ta ce amintatciyar hadimar ta wacce ita zata dinga kula da ita ta ƙwan ƙwasa mata ƙofa tace "Good morning ma Dr nusaiba tana zo duba ki, Rumtsai ido tayi ji take yawa ƙasan ta zai tsage tace "Mata ta same ni a ɗayan ɗakin , Okay ma a hankali ta tashi ta dafa bango ta nufi wata siririyar kofa ashe libta ce hawa tayi ta danna room 3 ai kuwa ta rufe da ƙar take iya tafiya yawa wata yar kaciya tsaya tayi ta buɗe a hankali ta fita samin Dr nusaiba tayi tana jiranta ganin irin tafiyar da take yi ta gane me ya faru zama tayi ƙwallah ta taro a idon ta Dr nusaiba tace "Sannu ya jiki ?, Kai ta rausayar tace "Da sauki amma wallahi ina cin azaba, Dariya tayi tace "Sai haƙuri da haka ko wacce mace ta girma , Hmmm kawe tace domin ta lamarin yanzu tsoro yake bata a haka su rufaida ke miƙa ƙansu ba lada sai zunubi we su ɗinga cewa a kwai dadi yanzu ta gane a she masifar rayuwa ce take ɗawainiya da su yo masifar rayuwa mana domin ita Bata ji wani dadi ba sai uwar azaba da tasha Yanzu zan duba ki mu shiga ɗaki ko A hankali ta tashi ta ta shiga bedroom dubata ta fara ta gano ashe ba ta farke ba saide gun ya daɗe allura tayi mata zata yi bacci inta tashi zata ji jikin ta yayi dadi sannan ta dinga shiga ruwan zafi shawarwari ta bata tun tana ƙasa da kai har ta saki godiya tayi mata Dr nusaiba tace "In wani abu ya shege miki duhu ga number ki kirani sai kin dage mata da yawa damar ki suke so basu samu ba kwalliya girki shagwaɓa kissa kisisina ƙarki yarda ko kunyi faɗa da shi ƙarki bari wani ya sani ladabi biyayya to wallahi ba boka ba malam zaki mallake shi iya kalami inyana tare da ke ki zame masa yarinya ke ko kinsan abu ki nunamai baki sani ba ko da yaushe jikin ki ya zamo cikin ƙamshi ki zame masa karuwa a gado zaki ga baya ke, Ƙasa tayi da idanuwan ta tace "Nagode sosai , Murmushi tayi tace "Wallahi anty zarah jinki naki kamar yar uwata gobe zan toro wacce zata dinga koya miki girki ƙarki yarda ma'aikatan gidan nan su dinga yi miiki girki ki dinga yi da kanki sannan ƙunshi gyaran kai a akai a kai zaki zamo yawa taurarowa a zuciyarsa , Kai ta jinjina mata domin we ita bata san irin auran da sukai bane ko kaɗan bata jin son a zuciyarta yanzu da zata sami dama guduwa zatayi taje ta sami rufaida domin tasan yanzu duk inda taje ta dawo dan wallahi sai sunyi kare jini biri jini tin da ita maciyiyyar amana Ni kuwa nace hmmmm rufaida ba yarda kika santa a da bace yanzu duniya ta canza ta tashi tayi zata raka ta tace "Nagode ki zauna keda baki da lafiya yanzu allurar zata ɗauke ki fita tayi kwanci tayi ta hade ƙafafuwan ta domin ko ya iska ta shiga zafi take ji haka bacci ya ɗauke ta wannan kenan Wasu irin manyan motocine ke shigowa bakake yau ko wanne ma'aikaci ya kwana da sanin yau mahaifiyar shugaban kasa zata zo wani irin mugun tsaro ake bawa gidan fitowa tayi cikin shiga ta alfarma leshi ne dan ubansu ta sanya lufaya sai ƙamshi take zubawa wasu yan mata be su hudu suka fito suna taku ɗaɗɗai sai wata kallo ɗaya za kai mata kasan ƙanwar Hajiya Turai ce Saboda yanayin da suke da ita ruƙe da hannun yusrah sai cin magani take babban floor aka shigar da su table ne dogo ba kayan motsa baki da ba a ajiye ba kama da na ƙasar nan zuwa kasasan ƙitare ko wacce zama sukai Ramlah ce ta ɗanci wani abun amma duk kansu sun wani haɗarai ganin wannan wacce irin ishashshiyar mata azzam ya aura mahaifiyar mijinta ta zo bata zo gaisuwa ba MOMCY ta dubi Hajiya Turai cikin salon munafurci tace "Wannan wacce irin mata ɗana ya aura ne iyayen mijinta da yan uwansa sun zo amma ba gaisuwa sai ma shanya mu da tayi tab lallai mun iɓo ruwan dafa kan mu nan gaba ma ganin ɗan mu sai ya gagare mu , Wani tuƙuƙin bakin ciki ne ya ziyarci zuciyar Hajiya Turai tayi ƙwafa da sake tace ''kee zo , Cikin rawar jiki me aikin ta zo yana sanye da uniform na ma'aikatan gidan riga fara wando baƙi tace "Gani Hajiya , Numfashi ta fitar me huci tace "Ina matar gidan nan ?, Shiru tayi domin ita bata taɓa ganin ta ba tace "Wallahi ban san shashinta ba amma ɗazu naji ance bata da lafiya, Okay jiki Tashi tayi ta bar gun ana haka sai ga jiniyar dawowar shugaban kasar daga meeting cikin ta ƙun ƙasai ta yake shigowa floor Assalamu alaikum yan matan ne ka dai suka amsa amma momcy Hajiya Turai sun cika sunyi fam ganin damuwa a fuskar mahaifiyar sa shima ya shiga damuwa gaida shi da su Ramlah keyi be amsa ba security ɗinsa yayi mai alama da ya sallame shi briefcase ɗinsa ya ajiye mai ya fita zama yayi yace "Hajiya kunzo lafiya , A jiyar zuciya ta saki tace "Lafiya qalau ina matar gidan ko ban isa ta zo ta gaishe ni ba ?, Da sauri ya dubi momcy domin sai yanzu ya gane wa ya zugata tun ba yau ba yake karantar taƙunta amma muje zuwa ya ɗora ma wasu alamomi tambaya akan momcy ƙasa tayi da idon ta tace "Ɗana na same ku lafiya , A jiyar zuciya ya sauke ya ce "Lafiya qalau ya kwana biyu ?, Alhmdllh tace Mai da hankalinsa yayi gun mahaifiyar sa yace "Hajiya bata da lafiya na fita da huri na manta ban sanar da ita ba zuwan ku , Banza tayi mai kamu hannunta yayi yace "Hajiya be kamata kiyi fushi ba akan abin da baki san dalili ba a kullum ki kan yiwa ɗan adam uzuri Hajiya har abadah bazan taɓa auro matar da baza ta ga darajar ki ba wallahi Hajiya bata san kin zo ba kafin ya ƙara sa maganar sa sai gata cikin material pink colour me yarfin flower golden colour da blue kanta yaci gyara ta tubke shi ya zubo baya bata sa ɗan kwaliba sai mayafin kayan da ta yane kanta da shi a hankali take tafiya kallo ɗaya za kai mata kasan bata da lafiya komai nata ciwo yake idanunta sun ƙumbura tasha kuka har ta gaji yanzu ma abin da ya kawo ta nan dan wani abun zata ɗora domin bata yarda da ma'aikatan gidan ba ganin baƙi tayi da sauri ta zuɓe a ƙasa tace "Barkanku da zuwa kun zo lafiya?, Banza Hajiya tayi tana jifanta da wani irin kallon tsana ta ɗauke kanta tace "Ƙƴen ɗan muciji ba asali ga rashin tarbiya ke abun yayi miki yawa , Wani yahu me ɗaci ta haɗiya idanunta suka cika da ƙwallah a she mahaifiyar sa ce Duban Hajiya Turai yayi domin be taɓa zaton tsanar da tayi wa zarah takai haka ba ita kuwa momcy ji tayi wani farin ciki ya mamaye ta bata taɓa zaton huɗubar da take yiwa yayar tata Zatai saurin shiga haka su Ramlah jidda ce kawe taji ba dadi Hajiya Turai tace "Ina godewa Allah da bamu haɗa zuri'a da ke ba sai de aci ayi kashi ko da yake an zubar da ƙwayayan haihuwar a rariya kina yiwa ɗana sharri a she kece me bin maza anji kunya kina ɗiya mace kin zubar da ƙimar ki , Wani duhu duhu ta fara gani rumtsai idanuwanta tayi tace "Momy kiyi haƙuri , Wata tsawa ta daka mata tace "Kije can ki nemi mahaifiyar ki ni ban haifi yar tiktok ba kaf dangana ba yar tiktok , nikuwa nace hmmmm Ta shi yayi yace "Hajiya ki haƙuri ina zuwa shiga ɗaki yayi be dade ba ya fito hannusa ɗauke da blanket face face da jini be so ya tona sirrin shiba amma dan ya wanke zararsa akan zargin da ake mata ya ware shi yace..... "Hajiya wasu lokutan da dama abin da muke zargi ba shi ke tambata ba wanda baka zargi shi ke faru mu kasance musu yiwa ɗan adam kyakkyawan zato Hajiya kamar mutuwar abbane hannun mutane da dama yana cikin har wanda bama zato kuma na kusa da mu ne yanzu nasa a ɗauko min file ɗin sa nafara binkice a kansa Jikin Hajiya Turai ne yayi sanyi domin ta gane abin da ɗan nata yake faɗa mata daman bata bi shawarar zurfa'u ba da duk haka bazata faru ba ƙin da take mata cikin kaso 100 % sauran 50 tuni zuciyar su haseena tamkar ammu su bishara da yau ce ranar mutuwar su saboda baƙin cikin da suke ciki haka momcy itama taso ta ci-gaba da hura hutar ƙiyayya a tsakanin su amma bata karaya ba ga ƙaryar da boka yayi musu yace ba zai kusan ce ta ba ga shi ya ku sance ta jikin ta asanyaye ta juya ta fita da ƙƴar take iya takawa ga wani dishi dishi da take gani dafa bango takeyi Allah ne ya kawo ta ɗakin ta lafiya hausawa sunce danasi ƙiya daman bata amshi tayin su alhaji datti ba da yanzu tana cikin ɗangin ta gashi ba mutuncin ta ba kuɗin da aka bata tayi dana sanin shiga harƙar media da siyasa daman tana da damar goge duk kan wani video ta har na wayoyin mutane da tayi wasu zafafan hawaye ne suka shiga zubowa yawa an buɗe fanfo bataji tsayuwar shi ba sai ji tayi an dafata rufe idon ta tayi ta turemai hannu babbar rigar sa ya cire sai ya koma daga shi sai yar ciki sai wando ya kwanta yana kallonta yace "Zarah nalura daɗi kike nema ai ba sai kin zo ɗaki kina kuka ba ni a shirye nake, Buɗe idanunta tayi dan jin wannan rainin hankali irin nasa wanne daɗi ko kuma abin da yafi daɗi take nema juya mai baya tayi domin da tana da kafa bar mai ɗaƙin zatayi ji tayi yana wasa da jilal gashin ta cikin sauri ta tashi zaune tace " tun ɗazu kake ta kala ta da faɗa na yi maka shiru bacci nake so nayi amma ka hanani yi , Tashi zaune yayi yace "Bacci zaki bara in cire kayana sai kiyi a jikina ni de fatana Allah isa jiya na baki ajiyata, Ƙauda kanta tayi ganin har ya cire rigarsa tace "A jiya kuma a ina da yaushe ?, Janyo ta yayi yace "Bara in nuna miki a in da na Baki a jiyata, za mu bura tayi ganin yana ƙoƙarin buɗe mata riga tace "Wallahi na yafe ba sai ka nunaba dan Allah ka dena abin da kake kai fa yanzu kai ne wanda zaka tsawatar wa al'umma kai kuma kake yi duk ka canza wallahi , Duban ta yayi dariya ta so ƙubɓu ce mai saboda har ta fara gumi duk uwar a.c da take aiki yace "Uhmmm laifi ne dan nayi wasa dake inje office na ɗauko tension in dawo in duk ga haɗa rai da me zanji ai Yanzu ke ce abokiyar jin dadi na ?, Tashi tayi domin ita wallahi tsoro yake bata tace "To dan Allah ka nemo wata , Duban ta yayi yace "Kin tabbata in nemo wata ƙar in nemo kuma kizo muna samun matsala da ke ?, Ba tare da yin dugun nazari ba tace "Eh, Uhmmm kawe yake yace ya tashi ya zura kayan sa yace "Zo muje in gabatar miki da ƙanne na ki gansu wata ɗaya za suyi tare da mu , Bin shi tayi sun zo dai dai floor ya kamo ta duk yar da ta so ta ƙwace amma yaki bata dama domin so yake yau su kasa bacci ko wacce ta haƙura da shi sallama sukai kamar an muntsine su suka ɗago suna kallon su da ƙƴar jidda ta amsa saboda wani kishi da ya turnuƙe su zaunar da ita yayi a cinyar sa yace "Life partner wannan ita ce Ramlah na bata wasu shekaru yar kahuna ce , Ƙoƙari take ta sauka amma ba dama cikin jin kunya tace "Sannun da zuwa , Ba wanda ya amsa ta Ramlah kuwa tashi tayi ta bar gun haseena ma da tana da ƙarfin tashi ta shi zata yi ta bar gun Yace "Wannan ita ce YUSRA yar anty zulfa'u ƙanwar Hajiya ta , Kallo ta bita dashi ta rasa a ina ta santa tambas ta taɓa ganin fusƙar nan amma ta manta ina ta santa maganar da yayi ya katsai mata tunanin ta yace "Wannan Jiddah yar anty kubura ƙanwar abbana, Ga haseena yar uncle mansur ce YUSRA HASEEE RAMLAH JIDDA ga antyn kunan zarah ita na zaɓa a matsayin abokiyar rayuwata in kuka ɓata mata ƙamar kun ɓata minne kar ku duba ƙanƙantar shekarunta a'a girmana za ku gani domin nine ita ita ce ni Kai kawe suka ɗaga mai be da mu ba da rashin maganar su yace "Besty ga yan uwana ki ruƙe su kamar yan uwanki duk da nasan halinki bani da matsala da ke , Cewa tayi "Insha Allah , Wannan kenan Na shiga ukku Alhaji wannan yaron fa dole mu ɓatar da shi domin ƙwaɓar mu tana shirin yin ruwa fa Ƙar ki damu lokaci muke jira muna gab da saƙin bama baman mu mu hana shi sakat ba dai a.i.g ya ce min we ya sa a kawo mai file 🗃️ din nan ba Alhaji baka san waye shi ba wallahi duk abin da ya sa gaba sai ya cimma tun yana yaro haka yake wallahi ina jin tsoron kallo da yake mun Wata dariya ya saki yace "Wato kowa ya sani duk wanda ya sai rariya sai tayi zuba kina tunanin Allah zai bar mu ai kawe mu jirayi ƙar shan mu kinsan hakkin r...... Kafin ya ƙarasa ta katsai wayar gumi na yanko mata tambas komai na shirin bayyana Wannan kenan Tun ranar da ya gabatar mata da su basu ƙara haɗuwa ba saboda yan zu ya samo me koya mata karatun addini bata samin damar zama a floor ga wacce Dr nusaiba ta kawo mata domin koya mata girki duk wanda ya santa a da yanzu ya ganta ba zai gane ta ba saboda wani irin kyau da ta ƙara da cika shi kwa kamai na ta fiya dai dai baya samin lokacin zama saboda yanzu binkin kisan abban ya sa agaba lokacin da ya dawo tayi bacci kullum sai ya zo ya duba ta ta window saboda tana sa sakata a ƙofarta haka zaman su ya kasan ce sosai su jidda suka shiga hankalin su tun ranar da ya gabatar da ita agaban su yau kuwa tun safe take sheƙa amai ta rasa me ke damun ta riga da siket ta saka na atamfa super sosai ta amshi jikin ta komai yayi mata kyau ɗaurin nan tayi ture kaga tsiya ga wata sarƙar gold da tasa da zaben ta sai ƙamshi take bazawa yau kawe sai tayi sha'awar zuwa babban floor taku take ɗaddai taci kunshi ja da baki samun su tayi a floor ko wacce na danna waya sallama tayi musu ba wacce ta amsa a cikin su bata da muba ta sami guri ta zauna tace "Monica Monica , Cikin sauri ta zo tace "Ma gani me kike so?, Ya tsuna fuska tayi domin ƙamshin turaran da yusrah tasa tun ɗazu yake damun ta tace " Strawberry Cake nake so , Okay ma babu amma bara in Miki Buɗa baki tayi zata yi magana aikuwa ta shiga kelaya amai temako take nema Monica ta sa hannu zata kamo ta yusrah tace "Ƙar ki kus kura ki taɓa ta ɓace min da ga gani banza , Sum sum ta bar gun Ramlah ta taso tace "Shigiya karuwa wa zaki nunawa kinyi ciki , Haseena tace "Batta wata kila ba na yaya azzam bane, Na uwar kine Duk kansu suka juyo sun ji Muryar wanda basu taɓa tunanin jiba yace "Na baku minti ukku ko wacce ta kwaso kayanta ta tafi gidan ubanta ƙar inji ko gidan Hajiya kunje marasa mutunci, Wallahi Hannu yasa ya zabgawa yusrah mari yace "Wallahi tak kika ƙara cewa sai na lahira yafiki jin dadi , Barin gun sukai ɗagata yayi ya nufi shashin sa da ita wanke mata jiki yayi tun tana noƙewa har ta saki ƙwantar da ita yayi ya ƙira Dr nusaiba ya faɗa mata rashi lafiyar ta tace mai gata nan zuwa Zama yayi ya dube yace "Sannu Allah ya baki lafiya, Kai ta ɗauke ta ja duvet saboda wani irin sanyi da take ji fahimtar haka yayi ya kashe a.c kiran security ya gani da sauri ya ɗaga yace "Eh ta shigo, ya kashe sallama tayi yace "Shi go , Shigowa tayi tace "Brk da dare da fatan kana lafiya ya me jiki ?, Da sauki yace matsowa tayi tace "Sannu meke damun ki?, yun ƙurawa tayi ta tashi tace "Amai ne sai zazzaɓi da ciwon kai da tashin zuciya , Ɗan murmushi tayi domin nata ganin zargin ta ya kusan tabbata tace "Yaushe rabo ki da ganin period ɗin ki?, Ga banta ne ya waɗi tambas za'a kawo ta gidan nan tayi wanka to a ranar wannan ƙaddara ta faru bakinta narawa tace "Wata da ya huce ban ƙara gani ba yau wata ukku kenan , Okay yanzu zan miki test sai inga me ke damun ki in go robar nan kiyi fitsari ki kawo min zanje lab ɗin asibitin gidan nan in dubu Amsa tayi zuciyarta na lugude ta shiga tayi Dr nusaiba tace "Ina ganin kamar ciki ne da ita fa, Fitowar kenan ta ji zancan ta ihu tasa da sauri yayo kanta yace "Lafiya me ke damu ki?, Robar ta saki a ƙasa ta zame tayi zaman yan bori tace "Dr dan Allah gaskiya kike faɗi shikkenan na shiga ukku ?, Tuni ya harbo jirgin a bin da ya sata ihu yace "Sister ɗin ta fa take ban labari yau shera shidda bata haihuba sai yanzu Allah ya bata , Kallon sa tayi tace "We hakane Dr?, Ehmn hakane vani in tafi ina ganin kamar malaria ke son maki Miƙo mata tayi amsa tayi tai musu sallama yace "Sannu kinji Allah ya baki lafiya , Tashi tayi tace "Ni nasami lafiya kawe jikina ne ya kemin nauyi , Cikin matsanancin farin ciki yace "Ai dole ki ji nauyi saboda baki ɗaya bace, Duban sa tayi tace "Ban gane ba Ni ɗaya bace Ni da aljanune kake nufi , Kamota yayi ya rungume ta yace "A'a gani nayi kinyi ƙiba kin ga kuwa ai kin zama nauyin mutum biyu , Kwantar da kanta tayi saboda dadin da turaransa yayi mata tace .... "don Allah ka bani turaran ka yayimin dadi , Ɗago ta yayi yace "Zan baki amma da sharadi, Lumshe idanuwanta tayi tace "Na yarda ka bani , Ɗan ƙwalin kanta ya cire yace "Kin amince ko mai ne zaki yi ?, sosai abin da yake mata take jin dadi tace "Eh na amince bani , Sai kin mun zan baki Turo baki tayi tace "Mene zaanyi faɗamin , To kawo kunnan ki kiji Matsowa tayi yayi mata raɗa ture shi tayi tace ''na fasa bana so wallahi , Wallahi baki isa ba sai kin mun ganin bakin Amince ba Zumɓuro baki tayi tace "To ai ban san abin da kake nufi ba kenan na zata ko girki zaka sani in maka , Janyo ta yayi suka waɗa gado yace "Yarinya aikin ruga in Amince ba canzawa, Uhmm dai wallahi ai baka faɗamin ba nifa bani da lafiya To ai magani zan baki Ganin abin ya fi ƙarfina na ɗau yan matan kafa ta nayi waje Wannan kenan Sadiyyah Riyadh الرياض Tafiya ke cikin natsuwa duk da damuwar da take damun sa tsawan shekaru juya akalal motar sa yayi kan titin  King Fahd Road, kusa da olaya district kallo ko ina yake cikin natsuwa yawa me shirin gano wani abun gaban wani shago ya tsaya yayi parking ɗin motar shi gaban wani shago ya fito kallo ɗaya za kai mai kasan Balarabe duk wanda yake mazaunin Saudiyya yasan wannan waye domin sanan nan mutum ne yana sanye da farar jallabiya da hiramin sa kallor rigar jikin sa za kai kasan daga gidan da ya fito duk da mulki baya gaban sa ba shi da girman kai ko kaɗan kowa na shine sallama yayi a shagon cikin saurin tsohon ya taso ya amsa sukai musabaha cikin girmamawa yace "Yallaɓe ga guri ka zauna , Zama yayi yace "Ina fatan dai ka ganeni ?, Tsohon ya washe baki yace "Yace ɗan nan na gane ka mana ba kai bane yarima sahir bin tahir Abdul Aziz ɗaga king Tahir bin Abdul Aziz kazit , A zurfar hannunsa ya juya yace "Abu mus'ab ba wannan nake nufi ba ka gane wannan ?, Wani tsohon photo kallo ɗaya za kai mai kasan tsohon photo ne da ƙƴar ake iya gane fusƙar matar ciki yace "Ka yi aiki a ƙar ƙarshin hukumar fita da wayan da ba yan garin nan ba ku mai da su garin su ka taɓa mai yar da wata mata da ƙaramin ciki za iya gane photo nan?, Tsohon amsa yayi kurawa photo ido na shekara ta 2005 yayi yace "Tabbas anyi haka amma yanzu na manta ina muka Kaita saboda shekaru sun cimmun kaga kuma nayi ritaya kasa a ɗauko maka file ɗin 2005 ina kyauta zaton zaka ga komai tunda mu muna girmama bayanai bama sulhuntar da su , Amsa yayi yace "Nagode abu nashir, Tashi yayi zai fita abu nashir yace "Ranka ya dade mene a laƙarka da me photo nan naga kamar ba jinsin bani abdulaziz bin fu'ad kazit?, Lips ɗinsa ya ciza ya kalli tsohon zuciyar tana wani irin suya yace "Eh ba jinsin mu bace amma tana da alaƙa ta auratayyah da bani abdulaziz bin fu'ad kazit, Ɗana to me isa a ka fita da ita bayan an san cewa tana ƙar ƙashin gida me daraja irin gidan ku ko zaka iyaimin bayani yar da zan gane? Komawa yayi ya zauna ya ɗauko tissue ya cire glass ɗin sa ya goge idon sa yace 2005 Ta fiya nake a hankali cikin natsuwa a mota ta wata yarinya wasu mutane suka biyu tana gudu tana neman ɗauki tsayawa nayi na fito tuni mutanan suka koma shigar da ita mota nayi duban ta nake kallo ɗaya zaka san ba jinsin mu bace amma kyakkyawa ce bazaka kirata da baƙa ba amma bata kai hassƙen mu ba nace "Wa yannan su wane suka biyo ki, Ta gane abin da yake nufi da yake kafin a kawo su nan ankoya musu yaran larabci ƙanta a ƙasa tace "Aikatau aka kawo ni nan a she ba aiki a ke ba karuwanci aka kawo mu wasu har Bara ake turasu shine na saci hannya na fito ashe sun gani shine suka biyo ni, Ransa ne ya ɓaci daman yana jin labarin nan ashe gaskiya ne yace "Ƙar ki damu insha Allah zaki koma gidan ku sannan zaki gane gidan ?, Ƙaita ɗaga mai tace "Eh zan gane , Yace ya sunan ki "Bilkisu ni yar ƙasar limon ce a garin ƙura , Kai tsaye gidan masarauta ya nufa duk da yana ɗar ɗar saboda yasan halin su yanzu nan labarin ya shigo da bare cikin masarauta zai baza Masarauta har ya kai gun sarki tsayawa faɗar ƙƴan masarautar ɓata baki ne parking yayi ya fito i tama ya ɓuɗe mata duk inda yasa ƙafar sa bin sa take ko ina ya huce gai da shi ake shashin sa ya huce da ita yace "Habibty habibty , Wata mata shiryar buɗurwa ce ta fito ta girmin ta nesa ba kusa ba hannunta ruƙe da yaro tace ''na'am hubby barka da dawowa ta rungume shi kowa dai yasan wannan a ɗabi'ar batarabeee gaisuwa ce bata kula da wata baƙuwar fuska ba ta zarce da yi mai kiss kaucewa yayi yace "Habibty tare muke da bakowa zan miki bayanin ta , Duban sa tayi cikin rashin fahimta tace "Wace wannan ?, Annuwar ya ɗauka ya farayi mai wasa ɗanne kishin ta tayi tace "Zo in baki ma sauki, Binta ta shiga yi wani madaidaicin ɗaki ta kaita ya ji kayan rayuwa zama tayi akan gado ta fito samun sa tayi baya floor bedroom ta nufa cewa ta tarar har ya shiga toilet yayi wanka zama tayi tana jiran sa annuwar yana gun me rainonsa data de kafin ya fito yana fitowa ta amshi towel tana gogemai jiki tace "Kai min bayani wace wannan ko hankalina zai kwanta ?, Kumatun ta ya ja yace "Sarah kishi ko , Uhmm kawe tace Bata labari yayi yace Ba zata daɗe ba za ayi binkice sai a mai da ita garinsu A jiyar zuciya yatayi bayan ya shirya ya fito suka ci abinci to bayan ya faɗawa king Tahir akai binkice ranar da aka gano gaskiya aka kama su a ranar aka fillemusu kai ko shurawa ba suyi ba ita kuma bilkisu za a mai da ita gidan nan fa yace be yarda ba zai aureta daga king har ummu maryam ba wanda ya yarda haka na saci hannaya na ɗauke ta naje wani ƙauye aka ɗauramana aure Muna zaune cikin jindadi har ta sami ciki sosai nayi murna nayi wa king ƙarya cewa ina wani kasuwanci ne haka sarah bata damuba kwana bibbiyu nake wa ko waccan su cikin bilki su ya shiga wata taƙwas wata ƙaddara ta gibta da yake ban mata igamaba ƙwasam ranar kwanan sarah na tafi ita kuma ta fito masu kama suka kamata aka dawo da ita garin su nayi kuka har na gaji dalilin haka nake fama da ciwon zuciya tun su ummu maryam na ɗaukar abin wasa har suka shiga tausayamin van da king gane yake hakkin sane ya kamani da tafiya tayi nisa ya haƙura ya yafe min tun daga ranar har kawo i yau ban ƙara sata a idona ba Abu nashir ya goge hawaye yace "A gaskiya na tausaya maka amma me zai hana ka bawa yan jaridun ƙasar limon cigiyar ta harda picture ɗin ta insha'Allahu za asameta, Godiya yayi mai sukai sallama ya fito Wannan kenan Kwana biyun nan azzam ya zama busy domin abubuwa sun mai yawa kullum yana hanyar yiwa mutane jaje yau a ƙona wannan gari a kwashe wasu daga cikin su ga case ɗin Abban sa Ita kuwa Binta tun daga Ranar bata ƙara yin wani laulayi ba sai abun da ba arasa ba sosai tayi wata irin ƙiba yau anty nusaiba ta kawo mata ziyara yira suke suka dariya tace "Anty nusaiba dan Allah ko zaki bani maganin tsutsar ciki wallahi kwana biyun nan damuna take ta dinga yimin motsi a ciki ga ciki na dayake kumbura , Dariya ce ta kusan kubɓucewa Dr nusiba ta yarda yaro ya yaro ne har kina tare da ciki wata hudu ki dinga cewa nutsar ciki ga alumu nan duk sun nuna tace "A'a ai kinga kinyi ƙiba ko dole duk wata ƙiba tana tare da tumbi ba cikin ki ne ya kumbura ba tunbine, Anty nusaiba wallahi baki ga yarda cikina yayi bane To zan aiko miki da magani bara in tafi ƙar oga yaga na daɗe Dariya tayi tace "To sai gobe ko , A'a bazan zo ba Marairaice murya tayi tace "Dan Allah anty ki dawo wallahi zama ni ƙadai ba yayimin dadi fa, To zan dawo har bakin ƙofa ta raka ta ta dawo bacci ne ya ɗauke ta bata san shigowar sa ba ji tayi an ɗauke ta fitgigit ta tashi batayi ƙoƙarin sauka ba sai ma kwanciya da tayi tace "Sannu da zuwa , Yauwa yace kawe domin ransa duk a ɓace yake a kan gado ya ajiye ta tashi tayi zaune ganin yanayin fusƙarsa ta ruko hannun sa tace " me ke damun ka , Zama yayi ya ruƙo hannunta yace "Yau an kama wayan suka kashe Ababana a she duk kisan mutanan da ake yi we duk saboda nine a gaskiya na fara tunanin barin mulki , A jiyar zuciya ta saki cikin da muwa tace "Alhmdllh Allah ya ƙara tonawa marasa gaskiya a siri yaya faɗuwar gaba a sarar namiji ne be kamata ka sauka ba ka ɗauko hanyar gyara , Rungume ta yayi yace "Ameen ya Allah ina godiya , Wasa ta shiga yi da hunnuwanta sun sha ƙunshi ja da baki kallon hannunta yayi yace "Yayi kyau sosai , Murmushi ta saki tace "Na tafi in kawo maka abinci , Bar abincin nan yanzu bana buƙatar sa zo ki tayani haɗa ruwan wanka Dariya ta saki tace "Wayo ko to wallahi yanzu ka denayi min wayo in shiga ka rufe da ni, Hmmm kawe yace wayar sa ce tayi ƙara da sauri ya ɗaga ita kuma ta fita dan ta gane me magana Hajiya ce sallama yayi Cikin alfahari da dan nata ta amsa tace "Allah yayi maka albarka yau ka cika min burina ita kuma ta je dan kanta tana yar uwa ta a haɗa baki da ita a kashe min miji hakkin rai ba zai bar ta ba , ameen ya Allah yace Hajiya Turai tace "Wani abun tashin hankali we yusrah ce take da ciki , Cikin rashin mamaki yace "Hajiya aini na taɓa ganin video ɗin ta nan ya shiga bata labari , Salati ta shiga yi tace "Kasan ita take zugani a kan matar ka a she ba ƙaunata take ba , Hajiya na daɗe da lura da haka Dan Allah ka nemamin afuwarta saboda haka wallahi bana son Ka kawo ta ƙunyarta nake ji Ba komai wallahi sallama sukai wanka ya shiga lokacin da ta dawo ta tarar baya nan yana wanka jere mai abinci tayi da sauri ta dafe cikin ta yau motsin da take jifi na koda yaushe ɗaga rigar ta tayi gabanta ya yanke ya waɗi hawaye ne suka shiga zarya a fuskar ta a haka ya sameta yace "Lafiya sweetheart?, Wani tuƙuƙun baƙin ciki ne ya tokare mata zuciya tace "Wallahi bazan yar da ba cikine da ni fa , Towel ya ajiye ya fasa goge jikin sa yace "Yanzu kukan da keke na mene na baƙin cikin kin sami zuri'a dani ne cikin jikin ki ba shege bane da ubansa , Tashi tayi yawa mahaukaciya ta fara dukan cikin ta roƙota yayi yace "FATIMA kina da hankali kuwa me kike haka me isa zaki guji jinana , Wallahi komai zaka ce min sai de ka cemin amma sai na zubar da cikin nan kuma ka sakeni bana son ka Jiyayi yawa an ɗugamai dalma a zuciyarsa yace "Yanzu me kikeso nayi miki inhar zaki barmin ciki na yakai har ki haifeshi nayi miki alƙawarin nemo miki abbanki , Tsayawa tayi cak ta dube shi tace "San nan zaka sake ni ko , Rintsai idanuwansa yayi da tasan yar da yake ji a zuciyarsa da batayi ba yace "Uhmmm sai ki nemomin wacce zan aura ko , Shiru tayi ta goge hawayanta tace "Ni bani da wata ƙawa ka nemo da kanka , Tunani ya shiga yi yace "Yauwa ga jidda sai in aureta, Ji tayi wani abu ya soki zuciyar ta tace "Ni zan je in kwanta , To ayi bacci lafiya maman baby Washe gari da sassafe ya fita office yana zaune muzamfar ya shigo gaisawa sukai yace "Naga kamar kana cikin da muwa pls ka faɗamin nasan ka da zurfin ciki barin maganar a cikin ka ba abin da zata amfanar da kai , A jiyar zuciya ya sauke ya faɗa mai komai ya ƙara da cewa Wallahi nayar da a kwace min komai na duniyar nan da na mallaka a barmin Hajiya da zarah kawe na faɗa mata zan saketa amma bazan yi ba komai kuwa zata yi Dariya yayi yace "Daman fa irin ku soyayya bata yi muku ruƙon wasa amma ga shawara itama tana sonka kawe batasan tana son Ka ba me zai hana in ka shiga gida ka dinga kirana ko Ni in kiraka muna yirar soyayya zaka ga yarda zaku ƙarshe da ita , Murmushin jindadi yayi yace "Allah ko , Yo mata ana rabasu da kishi ne kawe kai yarda nace kaga we yarima sahir yana neman wannan matar Da sauri ya ƙarbi wayar muzamfar ya fara kallo kamar su da zarar shi ta ɓaci yace "Annaya kuwa nan ba mahaifiyar zarana bace?, Kuma fa hakane nima naga kamannin su amma ka nuna mata ko Allah ne ya saukaka binkice Daukan komai yayi san nan ya bashi wayar sallama sukai ya fita Wannan kenan Hunin yau ji tayi gaban ta na waɗuwa addu'a ta shiga yi cikin ikon Allah sai ta dena kayan ta da yawa sun mata ƙadan cikin ta ya fito sosai wata irin yar kulawa yake bawa cikin ita kanta tana mamaki alamun shigowarsa taji tashi tayi ta tace "Sannu da zuwa , Yauwa yace mata abinci ta jera kan dining yau tuwan shinkafa tayi miyar agushi sai lemon Jinja sai farfesun hanta zuba mai tayi iya yarda zai iya ci ta zauna tana jiranshi fitowa yayi cikin t-shirt red da wando three quarter black colour kallon sa take yawa Ni ƙara kyau har yazo bata sani ba hannu yasa kamar zai tsone mata ido sauri tayi ta kau da ido yace ''nayi kyau ko video call zanyi da wacce muzamfar ya haɗani da ita ?, Wani ɓakin ciki ne ya turnuƙe ta ta furzo da abincin bakinta tafara tari cikin sauri ya kawo mata ruwa bayan ta dai dai ta yace "Me ya janyo miki haka at once kin ƙwari KO magana ta ce ?, Gir giza kai tayi tace "A'a zanje in kwanta , Kafin nan ina so muyi magana Komawa tayi ta zauna tace "To, Kinsan wannan amsar wayar tayi tuni hawaye suka fara tsaire a fuskar ta tace "Mama ce wallahi itace , Alhmdllh jibi zamu tafi Saudiyya sai mu nemo mahaifin ki Rungume shi tayi saboda jin dadi Wayar shi ce tayi ƙara ya dube ta yace "Kin ga ta kira yanzu nake tunanin ta a zuciya ta , Idon ta ne ya rufe ta kashe wayar yace "Ai yanzu lokaci na ne sai ka bari in ka fita kayi , Dariya yayi yace "Kince fa ba kƴa sona in ba so me ya kawo kishi, Wallahi ko me zaka ce sai dai ka faɗa Uhmmm bani wayata Ganin ya ɓat fuska jikin ta a saluɓe ta bashi Amsa yayi ya mai da aljihunsa washe gari yasa a Kai musu viza jibi suka tashi murna take tana farin ciki duk wata da muwar ta babu sai ta cikin jikin ta sauka sukai sun sami kyakkyawar tarba da yake ansanar wa da king Tahir bin Abdul Aziz kaxit ya tara kowa na gidan wasu irin hawayan farin ciki take Abbie ya rugumeta yace "Ina maman ki, Kuka ta sa tace "Ta mutu , Hawaye ya goge mata yace "Allah ya jikan ta amma tambas ya girgiza da jin wannan zance bayan taro ya watsai Abbie ya kama hannuta har shashinsa ya kaita Sarah an manyanta danne kishin ta tayi ta tarbeta tana janta a jiki binta mantawa tayi da azzam saboda tana cikin yan uwa ko shiru basa so tayi sun dinga janta da hira shima azzam kawe sai ya tafi yayi omara sosai cikin ta ya girma gobe zasu tafi abbie yaso ta haihu anan azxam yaƙi yau tana zaune mubinat da annuwar sun sa Binta a tsakiya sai yira suke mata wani tayi dariya wani tayi jimami haka Ummu Maryam ta same tace "Taso mu je shashi na , Binta tayi tana suna hira gyara irin na Larabawa ta shiga yi mata a kwana ɗaya duk ta can za washe gari ta fito zata yi sallama da kowa saboda jirgin safiya za su hau sun rabu da kowa ana ɗaukin juna number mu'azzam suka ƙarɓa ya ƙarɓi ta su a har airport suka rakota su sum bata kyaututtuka na ban mamaki Kanta ta kwantar a jikin sa tace "Nagode sosai da ka ci kamin alƙawari na , Ƙansa ya kauda yace Amsa yayi ya mai da aljihunsa washe gari yasa a Kai musu viza jibi suka tashi murna take tana farin ciki duk wata da muwar ta babu sai ta cikin jikin ta sauka sukai sun sami kyakkyawar tarba da yake ansanar wa da king Tahir bin Abdul Aziz kaxit ya tara kowa na gidan wasu irin hawayan farin ciki take Abbie ya rugumeta yace "Ina maman ki, Kuka ta sa tace "Ta mutu , Hawaye ya goge mata yace "Allah ya jikan ta amma tambas ya girgiza da jin wannan zance bayan taro ya watsai Abbie ya kama hannuta har shashinsa ya kaita Sarah an manyanta danne kishin ta tayi ta tarbeta tana janta a jiki binta mantawa tayi da azzam saboda tana cikin yan uwa ko shiru basa so tayi sun dinga janta da hira shima azzam kawe sai ya tafi yayi omara sosai cikin ta ya girma gobe zasu tafi abbie yaso ta haihu anan azxam yaƙi yau tana zaune mubinat da annuwar sun sa Binta a tsakiya sai yira suke mata wani tayi dariya wani tayi jimami haka Ummu Maryam ta same tace "Taso mu je shashi na , Binta tayi tana suna hira gyara irin na Larabawa ta shiga yi mata a kwana ɗaya duk ta can za washe gari ta fito zata yi sallama da kowa saboda jirgin safiya za su hau sun rabu da kowa ana ɗaukin juna number mu'azzam suka ƙarɓa ya ƙarɓi ta su a har airport suka rakota su sum bata kyaututtuka na ban mamaki "Bayan kin gujeni kin san irin azabtuwa da nayi ?, Kai haƙuri to sun sauka a filin tashi da sauka na Alhaji Ibrahim Bashir kura yan jaridu sun ci gun da jama'ar gari face mark ya bata tasa duk yar da yan jaridu suka so suji ta baƙin ta hakan ya gagara wasu irin manyan motoci ne daga fadar shugaban kasa a ka aiko su ɗauke su me maƙon su shiga gida sai ya sa aka juya aka lal motar zuwa gidan Hajiyar sa fitowa sukai yana ruƙe da hannunta gaban binta ne ya shiga lugudan uku uku bata san me zata tarar yau ba balle inta ganta da cikin nan ji tayi dan cikin ta yawani hautsulawa sauri tayi ta dafa cikin ta duban ta yayi yace "Lafiya me ya sami babyn?, Ƙasa tayi da idon ta tace "Ba komai , Kin tabbatar Eh har ƙasa ta ɗurƙusa tace "Hajiya ina huni, Cikin fara'a da ƙaunar ta ta janyo ta jikin ta tace "Zo nan ƴa'ta ƙun dawo lafiya ?, Ban Bara kwai taji we namiji da suna Hajara tace "Lafiya qalau, Zama yayi yace "Hajiya kin sami sabuwar ƴa'kin manta dani ko to wallahi sauka kar ki ƙarya min kafar ta, "Ba ruwanka damu yanzu kai ka girma , Tom shikkenan tonda haka kika ce Mu'azzam ya kamata kuje kura ko tun da komai ya huce itama taga yan uwanta da dan gin mahaifinka Duban hajiyar sa yayi bata san har yanzu ba zai iya sakewa da zarah ba har ya kai ta kura inta gudu fa yace "Insha Allah inta haihu sai muje , To Allah ya raba lafiya sai dare suka bar gidan a kwana a tashi ba huya agun Ubangiji yau tun safe Binta take naƙuɗa cikin hukuncin Allah Allah Ya sauke ta lafiya ta haifi yan ukku mace ɗaya maza biyu tuni labari ya baza duniya ranar suna macan taci sunan mahaifiyar Binta wato bilkisu ana ce mata afnan namijin yaci sunan baffa ana ce mai arfa ɗayan ya ci sunan abban azzam ana ce mai Irfan anci ansha an yi watsi da kuɗi yan Saudiyya ma ba abarsu abayaba sun zo tayata murna haka Hajiya Turai ta kashe dukiya asunan nan su Ramlah da hassena da Jiddah nayi aure sun zo suma domin har haƙuri sun bawa binta itama yusrah ta sami wanda yayi mata ciki ya aure ta sai de zaman baya dadi kullum cikin zargin juna yau dadi gobe ba dadi ga anyankewa momcy huƙuncin kisa yan zu ƙasar tayi lafiya tunda aka kama su Alhaji datti me tasa ƙasar tayi lafiya mulkin sa mutane na jindadi ilimi kyauta lafiya kyauta ga aiki baya huya washegarin sunan yarah binta ta dubi azxam yana yiwa yaran wasa tace "Ya batun maganar mu naji kai shiru ?, Duban ta yayi ya gane me take nufi amma sai yayi kamar be gane ba yace "Wacce magana kike nufi?, Jingina tayi da allon gado tace "Ta saki mana ai kaga na haife su ko daman haka mukai da kai , Kallon baki da hankali yayi mata yace "Ae sai na sami mata kuma wa zai raini su baffa kina so ki barsu cikin maraicin rashin uwa kina so suyi rayuwa ba uwa ke kin gujesu wacce macece zata kula da su bayan kin guje su kin san kuwa illar abin da kike faɗa kin san irin fushin da Allah zaiyi dake mutane da dama suna so su sami irin damar ki amma ke kin samu kina su ki fita daga cikin ci ta aure darajane ?, Hawayene ya zobo mata ta ɗurƙusa tace "Dan Allah kai haƙuri na ɗauki kaddara kai Allah ya zaɓa min , Bakomai Ni ba abin da kikai min wallahi Allah yayi miki albarka Ameen tace Wannan kenan Yara sun sami kula wa sunyi ɓulɓul abinsu sun je kura sun zaga dangi kahu labahani har kuka sai da yayi ganin irin kuɗin da azzam ya bashi haka Malam Umaru sosai yaji dadin ganin Binta ta kintsu kuma anga ubanta haka uwani da Maryam da saminu sai nan nan ake da binta kwanta biyu ta koma gidanta Bayan shekara biyu Yara sun girma sosai yawa ka ɗauke su ka gudu Binta ta buɗe wani foundation na tallafawa mara ƙarfi yau to asibiti zata je babban asibitin kura taje bangaren masu allurar ƙensa ta je ko wanne gado tabi tana bada dubu dari dari gaban wani gado taje da ƙar take iya shaƙar numfashi saboda warin da matar take afnan tana hannunta ta rungume cikin halin ciwo matar tace "Binta daman kece matar shugaban kasa ?, Har abada ba zata manta da wannan murya ba ya akai haka ta zama haka bakinta na rawa tace "Rufaida kece ko gizo kike min innalillahi ?, Kuka tasa tace "Wallahi nice ki yafemin Dan Allah nacu ceki ?, Hawaye ta goge tace "Wallahi na yafe miki duniya da lahira , Nagode sosai wannan ita ce yar tamu "Eh itace sunan ta afnan , Allah Sarki Allah ya rayata Ameen kuɗi me yawa ta bata inda tace a canza mata ɗaki ta ɗau nauyin kula da ita koda ta koma gida tunani ta shiga yi wato da azzam ya ji haushi ya sake ta bata san ina zata tsoma rayuwar ta ba sallamar shi ta ji da gudu ta rungume shi tace "Ina alfahari da kai miji na Allah ya barmu tare , Kuma tun ta yaja yace "Ameen yaran sane suka rungume su suna dariya, Alhmdllh alhmdllh Alhmdllh a yau na kawo karshen littafin Binta yar jagaliya ina yiwa Ubangiji godiya da ya bani iƙon gabama shi lafiya abin da na faɗa dai dai Allah ka bani lada abin da nayi kuskure Allah ka yafe min Duk da ban so gama littafin nan ba yanzu duba da zan fara jarabawa dole na kawo karshen sa Ina roƙon yan uwana musulmi addu'ar Allah yasa in fara jarabawata ta first semester level 2 asa'a