𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_Ɗan ɗano daga Zafafa biyar😋😋_* .........Kwanakin mako uku kenan da shuɗewar komai amma komai ya kasa mantuwa a zukatansu. Kuzari ya samu rauni kamar yanda dukkan karsashi ya gujema gangar jiki. Duniya ta masu ƙunci, ƙunci irin wanda har ƙarshen numfashi da wahala su manta. Farin cikinsu ya zama fansar damuwar wasu, wasun da kansu kawai suka sani basa kallon na ƙasa da su. Da ace ƙarfin iko a hanun kowanne ruhi yake a zahirin rayuwa, da ita ce zata zama mace ta farko a duniya mai ƙarfin ikon da zai girgiza zukatan kowaɗanne irin azzalumai. Kafin shuɗewar makwanni uku masu ɗauke da kundun baƙin ciki rayuwar ahalin Mal. Zayyan tamkar dutsen lu'u-lu'u suke a cikin tsakkiyar zinare. Ba magana ake akan dukiya ba, dan tana a cikin jerin abu mafi rauni da suke ɗauka ko amsa sunan ko kallo farin ciki. ana magana ne akan kammaluwar ahali masu matuƙar ƙaunar juna zunzurutu mara gauraye. Masu kuka a yayin zubar hawayen ɗayansu, masu dariya a yayin farin cikin ɗayansu, masu jiyya a yayin ciwon ɗayansu, masu zama komai a lokacin da komai yake abu ɗaya a hanunsu. 𝕽𝖚𝖒𝖆𝖓 babbar ƙasace a tsakkiyar wani babban tsibiri a wani ƙarni daya shuɗe kafin yau, ƙasace mai yawan arziƙin zinare yankin nahiyar Africa. Ƙasar Ruman nada babbar Daular mulki data ƙunshi manyan sarakuna masu ɗunbin tarihi kala-kala da labaransu bazai taɓa kasancewa shuɗaɗɗe ba a duniya. Ba arziƙin zinare ne kawai suke da shi ba, sunada nau'i-nau'in kayan itatuwa da wajajen noma harma da kiwon dabbobi da akan fita da su ƙasashe daban-daban ko'a shigo cikin ƙasar a saya. Al'ummar wannan ƙasa sun kasance wasu irin ƙyawawan mutane masu kwarjini da cikar haiba, sai dai duk da ƙyawun da mafi rinjayensu ke da shi hakan bazai hana a samu masu ƙarancin ƙyawun ba. Sunada yawan addinai da ƙabilu tamkar kowacce ƙasa, sai dai mafi rinjayen ƙabila sune masu yara yaren rumanci, sannan addinin musulinci yafi kowanne addini ƙarfi da rinjaye. Abu mafi mamaki a ƙasar ta Ruman shine, duk da ƙarfi da rinjayen da addinin musulinci ya samu suna girmama al'adunsu na kaka da kakani musamman ƙarfin iko. Ƙarfin iko nada matuƙar tasiri a ƙasar Ruman ainun, hakama al'adu da girman masautunsu na taka rawar ganin hana dukkan abinda turawa suka zo musu da shi taka rawar gaban hantsi a garesu bayan ilimin boko, duk da suma sun shiga cikin ƙangi na mulkin mallakar turawan a ƙarnin daya shuɗe. Babu wani mulki dake da tasiri sama dana sarautunsu tun a farkon ƙarnikan baya har zuwa yau ɗin nan da suke rayuwa bisa mulkin mallakar sarakunan dake mulkin mallakar su. 𝕯𝖆𝖚𝖑𝖆𝖗 𝕽𝖚𝖒𝖆𝖓 itace babbar masarauta da dukkan masarautu ke ƙarƙashin ikonta bama su talakawa kaɗai ba. Itace tamkar fadar shugaban ƙasa a wasu ƙasashe. A maimakon mulkin siyasa, su 𝐃𝐀𝐔𝐋𝐀𝐑 𝐑𝐔𝐌𝐀𝐍 itace babbar masarauta mai faɗa aji akan komai da kowa na ƙasar Ruman, komai yana tabbatuwa ko akasinsa da ƙarfin ikon sarki mai mulki a kujerar wannan daula. Bama gasu talakawa ba, babu wata masarauta a cikin kasar Ruman data isa koda ɗaga murya a bayan idon Daular Ruman saboda karfin ikon mulkin 𝐒𝐡𝐚𝐡𝐚𝐧-𝐬𝐡𝐚𝐧 (King of kings). Ƙarfin mulkin wannan Daula yakai a duk faɗi da ƙasar Ruman ke dashi babu wani mahaluki da zai iya faɗar siffa kai tsaye ko kamanni na sarkin da duk zai mulki daular ruman tun zamanin ƙarnikan baya, saboda tsantsar girmamawa da akema sarakunan wannan Daula ko iya ɗaga kai a musu kallon ƙurulla na kusa babu maiyi, daga nesa kuwa fuskokinsu ababen kwarjinine irin na masu mulki da a ranar wasan al'ada na kowanne shekara ake iya ganinsu a zahiri daga nesa bisa keken doki. A tsari da ƙa'idar daular ruman dukan yarima mai jiran gado daya shiga shekaru bakwai na girma za'a ɗaukesa kowa ya daina ganinsa, a sirrance zaiyi ilimin zamani dana addini dama duk wata rayuwarsa irin ta kowa. Bayan cikar shekarun girma a garesa za'a fara bayyanasa ga sarakunan sauran masarautu cikin shigar da ƙwayar idonsa kawai zasu iya gani. Nuna yarima mai jiran gado ga sauran masarautu na nufin alamar mahaifinsa zaiyi murabus kenan ya ɗaurasa a karagar mulki basai bayan ransa ba. Sarkin kuma da baya buƙatar hakan bazai taɓa bayyana yarima ba ga kowa har sai bayan mutuwarsa. 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐢𝐛𝐧 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐌𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 shine sarkin daular ruman daya shuɗe aka ɗora ɗansa ɗaya tilo bisa karaga. Shi kaɗai ya haifa a duniya, shine kawai magajinsa sai mata huɗu da saɗaka daya bari. A yanda tarihi yazo ba'a taɓa 𝐒𝐡𝐚𝐡𝐚𝐧-𝐬𝐡𝐚𝐧 mai ƙarfin iko da daularsa ta gagari duk wani jar fata nunawa yatsa ba kamarsa, ya shimfiɗa mulki a Ruman dama yankin Africa gaba ɗaya, izzarsa da ƙarfin mulkinsa yasa ba masarautun Ruman kawai ba, dukkan masarautun Africa na biye da shi da girmamawa da tsoro mai ƙarfi. Ya tara arziƙi mai ban tsoro da ban mamaki, ya kuma shimfiɗa ayyuka da ba Ruman kawai ba, Africa gaba ɗaya bazasu iya mantawa ba. Kaf ƙasashen jajayen fata masu faɗa aji na tsoro da shakkar 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐢𝐛𝐧 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐌𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝. Sarki Haysam ya raini ɗansa ɗaya tilo tamkar sauran shuɗaɗɗun sarakuna koma fiye da su, dan saɓanin sauran yarima da tarihinsu ya shuɗe shi wannan yariman tun a shekara uku na haihuwarsa babu wanda ya sake ganinsa kojin labarin inda yake rayuwa. Sai dai a kullum akanji sunansa a bakin Tajwar Haysam fiye da sau goma, ambaton sunansa shine mafi yawan magana dake fita a bakin Tajwar. Hakan kan saka razani da tabbatuwar shi wannan yarima zai kasance na daban a dukkan sarakunan da suka shuɗe kenan. Tabbas hasashen mutanen ƙasar ruman ya rabbata, dan kuwa dai kam da gaske 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 𝐢𝐛𝐧 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐦𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 ya zama sarki na daban a cikin dubban sarakuna, tare da labari mai ban tsoro da razani fiye dana mahaifinsa. Kamar yanda ƙa'idar daular ruman take bayan cikar shekara talatin da biyar yarima Eshaan ya bayyana a ƙasar haihuwarsa ta Ruman, sai dai kamar kowane yarima na baya babu mai iya ganin fuska ko suffarsa ta ainahi, hatta da idanunsa ma shi babu wanda zai iya ganin koda ƙwayar cikinsu sakamakon glass dake sakaye da su. Bayan gama bayyanashi ga masarautu da wata ɗaya kacal Tajwar Haysam bin Abdul-Majeed yay murabus aka ɗaura yarima mai jiran gado bisa kujerar mulkin daular ruman tare da auren mata huɗu galla-galla daga mabanbanta masarautu masu ƙarfin faɗa aji a kasar ruman. Kwanan 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 bakwai akan karagar mulki Tajwar mai murabus Haysam bin Abdul-Majeed ya kwanta jiyya, jiyya ce data girgiza kowa ta kuma bada mamaki, dan kuwa kwanansa ɗaya tak yace ga garinku nan. Kwatanta tashin hankalin da ƙasar Ruman ta shigama a lokacin bazai lissafu ba. Ƙura bata lafa ba mutuwar ɗaya daga matan 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 ta sake bayyana, kwana ɗaya da mutuwarta watama ta sake mutuwa a washe gari amare suka rage saura biyu. Al'amari ya fara saka zukatan jama'a hasashen da babu damar cewa komai. Wata biyu tsakani ɗayar matar ta uku ta sake mutuwa saura ɗaya. Tofa babbar magana. Abu mafi girgiza zukata shine mutuwar ɗayar data rage a shigar sabon wata. Kenan matan Tajwar 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 da mahaifinsa sun gama mutuwa kaf a cikar wataninsa uku da hawa karagar mulkinsa da kuma aurensa. Abun ya taɓa zukata aynun, sai dai babu wanda ya iya ko tari saboda tsoro. Sai dai abu mafi tsayawa arai a cikar wata na shidda aka sake ɗaura auren 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 𝐢𝐛𝐧 𝐇𝐚𝐲𝐬𝐚𝐦 𝐀𝐛𝐝𝐮𝐥𝐥-𝐦𝐚𝐣𝐞𝐞𝐝 da wasu matan biyu daga gidajen masarautun kasar ruman. Labarin bai canja ba, dan kuwa suma sun mutu ɗaya bayan ɗaya kafin cikar shekararsa guda da hawa mulkin. Abin al'ajabi aka kuma sake aura masa wasu biyun daga wasu masarautun, suma ɗin dai kamar ƙiftawar ido nasu labarin ya shuɗe a cikin shekara ɗaya. Haka aka sake ɗaurama Tajwar Eshan aure da wasu mata daga mabanbanta masarautu da tsoro bazai barsu hana auran ƴaƴansu ba, haka kuma suka mutu suma ya kasance duk ya auri yarinyar kowace masarauta goma da suke da su. Zuwa yanzu ba shakka da tsoron ɗaga murya bane kawai a zukatan mutanen ƙasar Ruman, hatta numfashi suna yinsane tamkar ɓerayen dake a ƙarƙashin tsaron maguna. A tunaninku yaya sautin fitar numfashin zai kasance?😭. ★★_________★★ Sunanta shine 𝕱𝖆𝖗𝖊𝖊𝖉𝖆𝖍 na yanka, sai dai iyayeta da dukan jama'a na mata alkunya da 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉. Su huɗu iyayensu suka haifa, itace auta a cikinsu. Hanash! Shine namiji babba. Arfa! ita ke bi masa, Fariha! Itace ta uku, sai ita auta 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉. Sunan mahaifinsu Zayyan!, amma suna kiransa Babiy, mahaifiyarsu Jamaima! Suna kiranta Ummu. Ƙasar Ruman ƙasarsu ce ta gado tun iyaye da kakanni, nan kaɗai suka sani, anan kuma kaɗai suke rayuwa. Kamar yanda na faɗa muku a tun farko ƙasar Ruman ƙasace mai tarin arziƙi nau-i daban-daban da ake kaikawo da su a cikin ƙasa da wajenta, tun daga kan zinare, noma, kiwo, ƴaƴan itatuwa dama wasu daban lissafo ba. Sai dai duk da wannan tarin arziƙi da ALLAH ya basu hakan bai hana kasancewar wasu a cikin matsayin talakawa ba. Kamar dai su 𝑰𝒇𝒇𝒂𝒉, mahaifinsu talaka ne mai rufin asirin ALLAH. Manomi kuma makiyayi, a nomansa harda noman zuma yakeyi. Dukkan wani nau'in zuma zaka samesa a hannunsa, wannan yasa yake mu'amula da daular ƙasar Ruman. Duk da ba masu arziƙi bane su mahaifinsu mutumne mai tsantseni da taka tsantsan, sannan ya tsaya tsayin daka wajen ganin sun samu ilimin addini dana zamani irin na yara ƴan gata. Gidansu gidane mai ban sha'awa da birgewa a ɓangaren mu'amulantar juna mai cike da soyayya da ƙauna. Basu da wani buri sai na faranta ran juna, a koda yaushe zaka samesu cikin nishaɗi dan talaucinsu bai taɓa kasancewa damuwa ga rayuwarsu ba ko nakasu ga farin cikinsu. Idan ɗaya na ciwo sukan kasance tamkar su duka suke ciwon, idan ɗaya na farin ciki sukan kasance su duka cikin farin ciki. Sune abokai kuma kawayen junansu harda iyayensu. Sunada tarin burika na rayuwa dana kai da kai, wasu a rubuce, wasu a ƙayyade a cikin zuciya, wasu a bayyane, wasu a adane a ƙasan zukata. wasu sun cika, wasu ƙaddarorinsu masu ɗaci da saka zubar hawaye dake gudana a halin yanzun sun yanke igiyar kaiwa ga samun cikarsu. Labarin sauyawar tasu, da yankewar tasu ya farane daga wata rana dake dai-dai da cikar sauran kwanaki huɗu na zagayowar bikin al'ada da ƙasar Ruman ke gudanarwa. Ranar da tarihinsu bazai iya gogewa ba, zukata bazasu iya mantawa ba, lissafin faruwarsu da shuɗewarsu bazai taɓa daina maimaita kansa ba koda a bayan rai ne.😭 A kowane karshen wata Babiy ke kai zuma tulu uku daular ruman, amma a duk bikin shekara na al'ada tulu goma yake kaiwa dan shi kaɗai ne yardajje a manoman zuma da sarki ke iya amfani da zumar dake zuwa daga hanunsa tun zamannin Tajwar Haysam. Koda ya mutu kuma 𝐓𝐚𝐣𝐰𝐚𝐫 𝐄𝐬𝐡𝐚𝐚𝐧 bai daina amsa ba. Sai dai kuma duk da wannan yarda a kullum zagaye suke da tsaro ta fannoni daban-daban duk a dalilin zumar da Babiy kan samarwa Tajwar. A ranar data rage sauran cika kwanaki huɗu na bikin al'ada rashin jin daɗin jiki ya saka Babiy bama Hanash damar tafiya dasu duka cikin ƙaton gidan gonat da yake noman zuma domin ɗurasu a sabbin tulunan da za'akai daular ruman. Da'ace yasan anjimarsa ko ƙaddararsa data ahalinsa da bazai taɓa barin wannan lokaci zuwa ba koda a mafarki. Sai dai kash, ƙaddara ta riga fata inji masu iya magana. Cike da farin ciki suka fita, dan kuwa a shekara sau uku kacal Babiy ke barinsu shiga cikin lambunsa. Ba lambun kawai ba, hatta fita koda ta zuwa makarantace suna yintane cikin shiga mai lulluɓe dukkan kamanni, domin kuwa ƴaƴan nasa na ɗauke da wani irin sirrin ƙyawu mai ɗaukar hankalin duk wanda zaiyi tozali da su, dan haka kullum cikin shigar larabawa suke harda niƙabi, idanunsu kawai ake iya gani da tafukan hanunsu, a yau kam sai suka fita a asalinsu batare da sanin iyayensu ba duk da kuwa suna dai sanye da abayoyin, sai dai babu niƙabin. Su kansu da'ace sun san abinda ke biye da rayuwarsu da zasu ninka niƙabi kan niƙabi ne har sama da sau sittin idan zai nisanta zuwan almakashin daya datse walwalin zinaren farin cikin zukatansu. Sun isa lambu sun gudanar da ayyukan da Babiy ya umarcesu cike da farin ciki da nishaɗi, suka tsinko tarin ƴaƴan itatuwa kowa da nasa da burin abinda zaiyi dashi a ranar bikin al'ada dake tunkarosu. shigarsu gida dai-dai da isowar tambura da bushe-bushen algaitu masu ban mamaki da al'ajab a cikin kunnuwansu dama dukkan sauran talakawan gari, dan abune da ba'a sabaji ba sai a wasu lokuta na gittawar Tajwar daga can kan hanya bawai a cikin anguwa kamar hakan ba...........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_2_* ...........Cikin ƙarfin hali Babiy ya zabura hanyar soro domin dubawa duk da halin ciwo da yake ciki. Baya yaja da sauri saboda cin karo da suka kusayi da tawagar jama'ar Daular Ruman dake ƙoƙarin shigowa suma. Kansa ya rissinar alamar girmamawa a garesu. Hanash da Ummu ma a kusan tare suka zabura. Cike da girmamawa mai haɗe da matsanancin tsoro Babiy ya zube bisa gwuyawunsa. Hakan da su Ummu sukaga yayi ya sasu zubewar suma tare da risinar da kawunansu, jikkunansu na matuƙar tsuma dan abune da ba'a taɓa gani kojin labarin faruwarsa a tarihin ƙasar Ruman ba. Babban mutum dake jagorantar tawagar ya tsaida idanunsa akan Babiy. “Ya kai wannan talaka dake a ƙarƙashin mulkin daular ruman, munzo da babbar magana ne gareka bisa umarnin daular ruman”. Ƙasa Babiy ya ƙarayi da kansa, tare da haɗe hannayensa waje guda. “Ina mai matuƙar farin cikin ganinku tare dani, ni mai biyayyane ga kowanne umarninku”. Duk da maganar Babiy ta musu daɗi babu alamar hakan a fuskokinsu. Ya miƙe cikin rawar jiki zuwa ɗakin Ummu. Mintuna kaɗan ya dawo da babbar tabarma sabuwa ƙal data saya domin auren Arfa zai shimfiɗa a gabansu. Dakatar da shi Shugaban tawagar tasu yayi cikin ɗaga hannu. *_“Munzo nan ne domin isar da saƙo ba zama ba ya kai wannan talaka dake a ƙarƙashin daular ruman. Umarni a gareka daga daular ruman, taga iri a gidanka kuma tana buƙata. Muna mai tayaka farin cikin zama ɗaya daga cikin surukan tarihin daular ruman”_*. A matuƙar firgice Babiy da iyalansa duka suka ɗago cikin zabura da matasanancin rikicewa. Sai dai basu da ikon koda motsa bakunansu balle neman ƙarin bayani. Kasancewar ba amsa dama suke buƙata ba mutumin ya janye idanunsa daga Babiy ya maida kansu Arfa da suka ƙanƙame hannayen junansu. “Wacece babba a cikinku?!”. Kalamai huɗu masu ƙarfin razani da neman fasa zukatan mai saurare da har abada bazasu bar amsa sauti cikin zuciya da ɓargonsu ba suka fita daga bakin ɗaya daga firɗa-firɗan samudawan dake zagaye da mutumin. Babu wanda ya iya motsawa a cikinsu, dan kuwa sake dulmiya suke a cikin duhuwa..... Saukar sautin wata zabgegiyar bulala mai adon jikin zakanya a jikinta ya sakasu zallo baki ɗaya. Babiy ya zube a ƙasa saboda azaba na raɗaɗin shigar wannan bahaguwar bulala a jikinsa, ganin basamuden mutumin dake riƙe da bulalar ya sake ɗagawa zai zuba masa Arfa ta miƙe tana mai fashewa da kuka jikinta na karkarwa tace.. “Nice!”. Cikin daka tsawa basamuden hadimin yaba Fariha da Iffah umarnin suma su ɗago. Ɗagowa sukai jikkunansu na karkarwa ga hawayen tausayin mahaifinsu ya wanke musu fuskoki. Idanu ya zuba musu kusan na sakan goma, kafin ya janye ya maida ga shugaban tawagar tasu.... “Zancenta nakan gaskiya ALLAH ya ƙara maka lafiya”. ya faɗa cikin girmamawa ga shugaban tawagar tasu. Shugaban ya gyaɗa kansa shima idanunsa akan Arfa “Mahaifinta da ɗan uwanta zasu zama waliyyanta”. Ya faɗa cike da cika umarni yana mai nufar hanyar fita batare da wani ƙarin bayani ba...... Har aka tafi da Hanash da Babiy babu abinda su Fariha suka fahimta, balle ma Iffah da kallon kowa kawai take. Kukan Ummu ne ya dawo da su hankalinsu, gaba ɗayansu sukai kanta. Ummu dake kuka kamar ranta zai fita ta haɗasu su duka ukun ta rungume jikinta na wani irin rawa...... ★★_______★★ Tafiyarsu da kamar awanni uku Babiy da Hanash suka dawo gida da doki ɗaya da tarin kayayyaki, sai rakuma guda uku. Fuskokinsu cike suke da firgici mai tsayawa a zukatan masu kallo. Ba abinda sukazo da shi bane a gabansu Ummu, burinsu susan mike faruwa? Kawai. Basu samu amsa ba daga garesu har bayan shuɗewar wasu awanni, kafin Babiy ya basu amsa cikin dakewa.... “Na bada aurenta ga *_Shahan-shan_*, bamu baro ba sai da aka ɗaura musu aure, wannan raƙuman da dokin sadakinta ne”. Ya ƙare maganar idonsa akan Arfa. Tamkar saukar aradu mai tarnatsa haka furucin ya isa cikin kunnuwansu, Ummu tai baya zata faɗi Babiy ya riƙota, kansa yake girgiza mata alamar kartace komai, suma yaran ya juyo garesu yay musu nuni da shiru ya jata suka shige ɗaki. Umarnin mahaifinsu shine mafi girman biyayyarsu garesa matsayinsu na waɗanda ke rayuwa a ƙarƙashinsa, badan sun so ba suka zaɓi shiru, sai dai shirun nasu bai hanasu haɗe kai a ɗaki suyi kuka ba su ukun. Kuka irin wanda za'a kira kuka a duk idaniyar da zubar hawaye ke kwaranya na rashin lissafin ƙididdiga. Mintuna sun shuɗe, hakama awannin da suka ƙarasa kalmashe wannan yinin. Bayan sallar magrib saiga motoci da tawagar hadimai tare da wasu hamshaƙan mata huɗu wai sunzo ɗaukar Amarya Arfa. Kuka suke tamkar ransu zai fita, haka sunaji suna gani suda iyayensu aka shirya Arfa cikin shiga ta alfarma aka wuce da ita Daular Ruman. Dare ya riski zukatansu cike da damuwa, yayinda sai ɓarawo mafi iya satane ya samu nasarar sama musu nutsuwar wucin gadi wato barci. Sun wayi gari kunnuwansu a buɗe na jiran jin labarin mutuwar ƴar uwarsu, sai dai babu wani alamar hakan har sake shuɗewar kwanakin zuwan ranar bikin al'ada. Babu fashi aka gudanar da bikin al'ada na ƙarshen kowace shekara. Sai dai su a zuri'arsu babu wanda ya leƙa koda ƙofar gida. Anyi an gama, kamar kowace shekara an samu rashin rayuka a wasanni daban-daban, da kuma haɗarin mota dana mashina suma a tituna daban-daban saboda cinkoson jama'a dalilin garin shine babban birni da Daular Ruman ke ciki. Bikin al'adar ƙasar ruman kuma yana ɗaya daga cikin biki mai tsananin ƙayatarwa da mutane daban-daban suke halarta daga sassan duniya ta ko ina. Shahan-shan ya fito zagaye tamkar kowace shekara cikin shiga ta alfarma, bashi a karan kansa ba hatta keken dokinsa ma abin kallo ne, sai dai a wannan karon ma babu wanda zaice ga kamanin Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed ɗin. ★ A haka lokaci ya ƙara turawar da kwanaki suka zama watanni kusan uku. Shuru na waɗannan watanni bai sama musu wata nutsuwa ba, dan a kallon farko da mai gani zaima gidansu zai san akwai matsala tattare dasu. Komai ya sauya, sauyawa irin wadda ƙaddara ta shigo cikin tarihinsu. Babu mai walwala a cikinsu, komai na ƙarfin hali sukeyi, abinci ya gagara ciyuwa yanda ya kamata a koda yaushe garesu, sai cin ƴaƴan itatuwa, tunkan a sanar musu alamominsu sun tabbatar da zaman makokinsu. A haka duhun wani dare na cika watanni uku da kwana uku da auren Arfa ya sake riskarsu, suka sake zama ƙarƙashin mulkin mallakar ɓarawo mafi iya sata koda shiri ko babu wato (barci). Daren da yazo ma Iffah da wasu irin munanan mafarkai masu firgici daban tsoron. Har rige-rigen fitowa suke daga ɗakunan barcinsu sakamakon fitar sautin razananniyar ƙarar data karaɗe gidan mai ban tashin hankali. Su duka huɗun suka rufu a kanta kowa na ambaton sunanta da kai hannu jikinta. Duk da sanyi da akeyi jike take sharkaf da zufa ga illahirin jikin nata daya ɗauka zafi. Ummu ta rungumeta tana mai sakin hawayen da ke kwance a cikin idanunta. Ta riga ta farka dan haka itama ta ƙanƙame Ummun tana fashewa da nata kukan. Ba yau ne karan farko da Iffah ke shiga irin wannan tsoron ba sakamakon firgici a mafarki, sai dai na kwanakin nan yafi razanarwa da saka ruɗani a zukatansu. Babiy ya kai hannu ya shafa yalwataccen gashin kanta, murya a raunane yake ambatar sunanta.. Kanta ta ɗago a hankali fuskata sharɓan da hawaye, ta dubi mahaifin nasu da Yayansu Hanash da Fariha, sassanyar ajiyar zuciya ta sauke tare da haɗiye sauran kukan tana tashi zaune daga jikin Ummu ta share hawayen dake jiƙe da fuskarta. Matsawa tai jikin mahaifinsu tana mai kamo hanunsa. “Babiy inajin tsoro, matuƙar tsoro a wannan mafarkin fiye dana kullum. Babiy itama Nina Arfa kashemana ita zasuyi kamar sauran matan daya aura?, itama zamu rasata na gani a mafarki na...” Da sauri Hanash da dukkan rauninsa ya bayyana a fuskarsa ya shiga girgiza mata kansa cikin aro jarumta. “Mafarki ba gaskiya bane Iffah, ki kwantar da hankalinki Arfa na cikin ƙoshin lafiya tamkar mu insha ALLAHU...” “Amma Akh Hanash nawa yasha zama gaskiya, a daren da Nina Arfa zata bar gidan nan irin wannan mafarkin nayi a kanta, yau ma shine na maimaita da ita babu banbanci a cikinsa na rantse maka”. Har ƙasan zukata zancen nata ya dake su, ganin bayyanar rauni a fuskokinsu ya saka Babiy yin murmushin ƙarfin hali yana shafa kanta. “Shaiɗanu zasu iya dawo miki da makamancin sa ai Ibnati, dan haka ki kwantar da hankalinki Arfa na lafiya a gidan aurenta”. Bazata cigaba dayin jayayya da su ba, amma tana cikin matsanancin damuwa tamkar yanda take hango tasu akan fuskokinsu. Maimakon komawarsu barci sai duk suka miƙe zuwa tsakar gida, alwala suka ɗauro, suka koma can runfar dake matsayin falon iyayensu suka fara salla da miƙa kukansu ga UBANGIJIN talikai da fatan hana tabbatuwar abinda zukatansu ke cikin tsananin fargaba. Haka suka kasance har sallar asubahi gaban mahaliccinmu, bayan idar da sallar asubahi maimakon kwanciya sai suka riski kansu a zaman jugum-jigum na jiran tsammani. Har fitowar rana babu wani yunƙuri daga ɗayansu. Sai ko ga isowar abinda suke fargabar ya riskesu ya iso garesun. Shigar bugun gidan a cikin kunnuwansu ta sakasu miƙewa a zabure gaba ɗaya kuma a lokaci ɗaya, kowanne cikin rawar jiki da fidda tsammani. Babiy ne yay jarumtar ƙarasawa ga soro cikin jan ƙafa. Tunda yay tozali da hadiman masarauta zuciyarsa tai wata irin masifar wulƙitawa..... “Kun kasheta itama ko?!”. Da shi da hadiman suka riski muryarta a cikin kunnensu a bazata. Sam babu tsoro ko shakka irin wadda akema duk wani mai alaƙa da masarauta a ƙasar cikin idanunta a yau. Sun soye sunyi jazur irin na tashin hankali. A harzuƙe cikin hadiman ɗaya ya daka mata tsawa da faɗin, “Hattara ɗiyar talakawa, bakin rijiya ba wajen wasan yaro bane”. “Idan yaron ya kasance rago ba!!”. Ta bashi amsa itama a tsawace. Shimfiɗeɗiyar bulalar hanunsa ya ɗaga zai zuba mata Babiy ya kare cikin rawar jiki yana mai zubewa ƙasa a kan gwiyawunsa. Sosai a zaba ta ratsashi, ya rimtse idanu cikin aro dakiya da jarumtar dole, “A gafarceta ita ɗin yarinyace masu nasara”. Ya faɗa cikin rawar murya saboda azabar tasirin shigar bulalar. Ƙasa Iffah takai durƙushe gaban Babiy tana mai fashewa da kuka, kafin ta ɗago ta dubesu zatayi magana Babiy yasa hannu ya rufe mata baki jikinsa na tsuma. Jikin nata itama tsumar yakeyi, sai dai ita bana tsoro bane na tsananin baƙin ciki ne da bushewar zuciya. So take ta amayar da abinda ke bakinta an hanata. Batare da hadiman sun sake bi takantaba suma suka isar da saƙon dake tafe da su. “Kasancewarka mai biyayya da bin umarnin masarauta a karo na biyu an sake baka damar halartar jana'izar ɗiyarka kai da zuri'ar ka. Mun barka lafiya”. Innalillahi wa-inna'ilaihirraji'un. Babiy ya shiga ambata, kusan a tare Ummu da Fariha suka saki razananniyar ƙara wadda ta jawo hankalin maƙwafta da mutanen dake tsaitsaye a ƙofar gida tun wucewar hadiman masarauta. Dan sun san dai labarin gizo bazai wuce na ƙoƙi ba........ *_WASA FARI GIRKI_* Dole ne zuri'ar mal. Zayyan su ambaci rasuwar Arfa da kalmar WASA FARIN GIRKI a jerin zaren ƙaddarar da ta kutso a rayuwarsu mai ɗauke da almakashin da ya datse farin cikinsu. Sun rasata tamkar labarin hikayoyin marubuta ko wasan kwaikwayo na film. Ta tafi tafiyar da bazasu sake ganita ba, tafiyar da babu wanda aka bawa damar yin cikkakkiyar sallama da ita a cikinsu hatta mahaifansu. Ta shuɗe a ƙaddararsu tamkar yanda ruwan damuna kan tafi da duk wani yayin dakan tare masa hanya a lokacin wucewa. Komai ya faru tamkar ba'aiba. Babu mai iya koda tari balle bin ba'asi. Iyakarsu kukan idanu dana zuci wanda muryarsu kan tsayane kawai iya filin gidansu ko katanga basu isa bari ta haura ba. A yau ma dai Babiy da Hanash ne sukaje domin jana'izarta. Suko aka barsu da amsar gaisuwa a cikin gida wadda mutanensu talakawa na zuwa musu itane a ɗarare....... Kwanaki sun cikagaba da shuɗawa tamkar ba'ai komai ba, yayinda ɗayar matar Tajwar da aka aura masa tare da Arfa itama dai ta mutu bayan wasu watanni. Bayan su Arfa ba'a sake jin Tajwar yayi wani aure ba, sai dai mutane na raɗeraɗin a duk randa aka kaisu domin ziyartar turakarsa babu fashi gawarsuce take fitowa. Hakan yasa kowa ke danganta mutuwar matan da tsafi yakeyi dasu. Wata huɗu da sati ɗaya cif tarihi ya sake maimaita kansa, dan kuwa Fariha ta sake faɗowa a jerin matan da aka ɗaurama Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed aure da su. Batare da wani shawara ba a safiyar alhamis suna zaune kira ya riski Babiy daga masarauta, babu wanda bai shiga tsoro da firgici ba a cikinsu, sai dai babu wanda ya isa hana hakan a duk faɗin ruman. Sunaji suna gani babiy yay shiri ya amsa kiran. Tafiyarsa da awanin da basu gaza biyar ba sai ga hadiman masarauta sunzo sunma Fariha ɗaukar amarya itama babu wani bayani daga garesu. Ranar dai kam Iffah bata gazaba kojin tsoro wajen gwada musu hauka, dan bata bari an fita da Fariha ba har sai da basamuden nan ya zabga mata bulalar dorinar hanunsa data sakata zubewa, bata tashi dawowa hayyacinta ba sai bayan wucewarsu da kusan awa guda. Zuwa lokacin har Babiy ya dawo. Kamar dai Arfa itama Fariha an ɗaura mata aure da sarkin da kowa yake masa inkiya da fir'aunan wannan ƙarnin. Sai dai a ɓoye wannan suna ke fita a bakunan talakawan gari irinsu Iffah. Sakamakon bulalar da aka zabga ma Iffah bayanta yay mugun fashewa har akan mazaunanta, ga wani raɗaɗi mai azaba na ratsata har ta kasa riƙewa sai da ta saki ƙara. Babiy da Ummu suka rufu a kanta, hawaye suke suna jeramata sannu, Hanash na gefe zaune idanunsa jajur alamar tsananin ɓacin ran da babu ƙarfin ɗaukar mataki...... Tayi jiyya ta kwanaki uku, wajen ya warke, daga haka kwanaki suka cigaba da tafiya, inda a cikar watanni biyu itama Fariha mutuwarta ta riskesu tamkar ba'ayita ba. Sun sake rasa Fariha a dalilin auren Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed........✍😭 *_Hummmm!!😕🤌🏻_* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafarta ma iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_3_* _____________ _*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_ _*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._ _*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._ _*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_. _*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._ _*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._ _*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_ _*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._ _*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ *_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._* ______________ .........A wannan gaɓar haukane kawai ya rage wannan ahali suyi, dan duk dauriyar Babiy ya kasa danne raɗaɗi da zafin da yakeji. Itako Iffah kalaman dake fita a bakinta kausasa sun saka kowa ke ɗaukar tama zare kawai. Daga ƙarshe maganin barci aka ɗura mata. Bata tashi farkawa ba sai a ƙauyen da kakanninsu ke rayuwa. Wato iyayen Ummu. Rayuwa a ƙauyen Jumna a gareta tamkar mai gushewar hankali ya zame mata. Domin bata gane komai sai sambatu da kalamun ɗaura ɗammarar ɗaukar fansa ga duk ahalin Daular Ruman. Ba ƙaramin dagewa da jajircewa kakannisu da su Babiy sukai ba a kanta wajen ganin ta samu lafiya ta dawo hayyacinta. A cikin watanni takwas ta rasa yayunta guda biyu, wannan babban tarihine da bazai gogu a zuciya da ruhinta ba har karshen rayuwarta. Bayan jiyyar watanni kusan uku ta dawo hayyacinta. Sai dai ta daina fira'a da kowa, an daina ganin dariyarta ko farin cikinta. Babu abinda ke'a ranta sai buri da ƙudirin ɗaukar fansa. Tama kanta alƙawarin ita da hannunta zata kashe *_Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed_*. Bayan nan idan itama an kasheta burinta ya cika na kawar da azzalumin sarki mai mulki irin na fir'auna a ƙasarta a cikin al'ummarta.... *_(Babbar magana. Tayaya wannan buri naki zai cika Iffah😱? Sarki mai cikakken iko irin Tajwar Eshaan, mai amsa sunan Shahan-shan da ko fuskarsa babu wanda ya iya sani a cikin kasar Ruman har yanzun. Anya kuwa....? To mudaije zuwa wai mahaukaci ya sai kura😬🤧🚴🏼)_* ★★★ “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” bakinta ke ambata cikin firgici da rawar jiki sakamakon farkawar da tayi daga mummunan mafarkin daya risketa a cikin barcinta. Ta dafe kanta dake wata irin sarawa na ciwo tamkar ana mata luguden taɓaren daka a tsakkiyarsa, gaba ɗaya jikinta ya jiƙe da zufa tamkar tayi wanka. Kusan watanni biyar kafin mutuwar ƴan uwanta da fara canjawar salon mafarkainta saɓanin na baya, abu mafi tsoratarwa kuma kusan mafarki ɗaya ne ke maimaita kansa a kowane barcinta idan ta kwanta. Sai dai mafi tashin hankalin a yau yayi kamanceceniya da na wasu dare da tarihi bazai taɓa mantawa da shi ba a cikin rayuwarsu ita da ahalinta. “Nina Arfa! Nina Fariha!”. Ta ambata a zahiri zuciyata na ƙara ƙarfin gudu, yayinda hawaye suka shiga rige-rigen sauka a kumatunta. Tabbas irin wannan mafarkin tayi a daren da suka rasa Arfa, hakama daren mutuwar fariha. Yau kuma gashi ta maimaitashi akan kanta. Itama kenan zasu rasata?. Kai ta shiga girgizawa wani kuka masu ƙarfi na sake tahomata, hannu tasa ta toshe bakinta gudun kar sautinsa ya kai ga kunnen kakanninta. Sai dai aikin gama ya gama. Dan kuwa muryar kakanta takeji jikin ƙofar ɗakin nata a hankali yana ambatar sunanta. Da sauri ta shiga goge hawayen, kafin ta tashi daga shimfiɗar barcin nata wadda karan gado ne da katifar rimi. Mayafi ta ɗauka ta yanama jikinta, ta ƙarasa ga ƙofar ta buɗe... “Kina lafiya kuwa ɗiyar nan?”. Ya faɗa cikin kafeta da idanu. Kanta dake rissine ta jinjina masa, cikin son danne kukan dake yunƙuromata ta bashi amsa. “Ina lafiya Kaka”. Jin shiru bai sake cewa komai ba ta ɗago ta dubesa a karon farko. Shima dai kallon nata yakeyi tamkar mai nazari. Sake maida idonta tai ƙasa, hawayen da take faman riƙewa suka ɓalle mata da gudu. Bata san ta ambaci “Kaka nima zasu kashe muku ni ko?. Inaji a jikina nima zaku iya rasani nan kusa tamkar yanda muka rasa su Nina Arfa”. Rawar da jikinta ta fara ta sata zubewa a gabansa kuka na ƙwace mata. Kusan minti biyu baice da ita komai ba, ita kuma ta kasa tsaida kukan.. Jin saukar hanunsa saman kafaɗarta ya sata haɗiye kukan, ya ɗagota tsaye yana ɗan murmushi dake sake bayyana tsufansa. Gefen mayafin jikinta ya kama ya shiga goge mata hawayen. “Fareedatu! Ki kwantar da hankalinki, insha ALLAHU babu abinda zai faru da ke, mafarki ai ba gaskiya bane ba. Suma su Arfa kwanansu ne ya ƙare, koba komai kuma sun rasu a gidan aurensu. Wannan kawai ya ishemu farin ciki”. Kanta ta jinjina masa tana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Ya cigaba da shafa kanta a hankali har zuwa wani ɗan lokaci. “Kije kiyi addu'a ki kwanta abinki da safe zamuyi magana”. A hankali tace, “Kaka ina son zuwa naga su Ummu gobe to dan ALLAH”. Da sauri ya girgizamata kansa. “A'a bazai yuwu ba Iffah, iyayenki sun kawoki nan ne domin kuɓutar dake, taya kike tunanin zan barki komawa cikin daular Ruman?. Tun ina ƙanƙanin yaro nake bauta wa masarautar Ruman, bayan mutuwar mahaifina na cigaba da bautar saƙa kayan doki a garesu kamar yanda mahaifina ya barmin gado, a haka na haifi ƙanin mahaifiyarku shima ya mayeni, gashi har girma ya riskesa shima yana bauta musu. Mun rasa ɗan uwan mahaifiyarku a yaƙin kare daular Ruman, mun rasa Arfa, da Fariha. Ke ɗaya da kika rage mana da yayanki wajen mahaifiyarku kuma sai muyi wasa da rayuwarki? Bazai yuwuba jeki kwanta...” Batare daya sake bata damar yin magana ba ya juya ya koma bayan ya jamata murfin kofar. Da kallo kawai ta bisa hawaye na silalo mata. Duk yanda taso komawa barcin bayan tafiyarsa hakan ya gagara, zuciyarta ta kasa fita da ga ƙangin fargaba, da gaske tanajin matuƙar tsoro bayan rasa Fariha da Arfa da sukai watanni ƙalilan da suka shuɗe itama su rasata, tanaji zuciyar ahalinta bazata iya ɗauka ba idan itama suka rasatan. Wasu zafafan hawaye suka sake silalo mata masu raɗaɗi da saka ƙuna a ƙirji...... ★★★ “Iffah! Iffah!!.....” Sautin ƙwala kiran sunanta daga muryar kakarsu da suke kira Iyyani ya sakata fitowa daga banɗaki data zagaya domin yin fitsari. Turus ta tsaya tare da haɗiye maganar da zatayi tana mai kallon ɗan-uwanta Hanash dake zaune gefen kakar tasu a ƙarƙashin bishiyar ɗoruwa da take a tsakar gidan. Murmushin da yakemata ta maida masa, kafin ta ajiye butar hannunta ta ƙarasa garesa. Dab da shi ta zauna tana mai ɗan rungumesa ta gefe da faɗin, “Ina kewarku Akhi”. Murmushinsa ya sake faɗaɗa yana mai kallon fuskarta. Ya kai hannu ya shafi yalwataccen gashin kanta da mayafin ya zame mai tsaho da santsi. “Muma muna kewarki Little angel. Gidan duk ya sake zama mana babu daɗi”. Yanda maganar tasa ta ƙare cikin rauni itama sai idonta ya cika da ƙwalla. Amma sai ta dannesu da murmushin mai ɗaci tana kaɗa kanta kawai. “Tashi ki bashi ruwa mana, k haka ake tarbar baƙo a garinku”. Baki ta ɗan tura gaba da kallon Iyyani mai maganar, tayi hakane danta katse raunin data hanga a fuskokinsu. Ta miƙe tana bata amsa cike da shagwaɓa. “Iyyani laifinkine fa, ban taɓa ganin matar da bata tattalin mai gida ba irinki, dole Yayana ya miki kishiya”. Daƙuwa tamata cikin gatsina fuska. “Ungo naki nan Fareedah, yo bandama lalacewa mizanyi da wannan faratun mai kama da jar tsada tuzurin banza”. Hanash ya tsuke fuska yana kallon Iyyani. Murmushi Iffah tayi tun kafin ya faɗi abinda ke bakinsa. Dan dama inhar suka haɗu da Iyyani sai ta hasalashi take jin daɗi shi da Arfa akan ƙinyin aure, duk da bawani shekarune da shi ba, dan ashirin da shida ne kawai, Arfa nada ashirin da uku, Fariha nada ashirin da ɗaya. Iffah nada goma sha takwas.... Iffah ta dire masa abinci da ruwa ta sake kaiwa zaune kusa da shi sannan ta dubesa. “Akhi yasu Babiy suke?”. Ya nisa a hankali bayan ya dire moɗar ruwan daya sha. “Duka lafiya suke. Suna gaisheki ke da su kaka. Duk da suma dai nan da kwana kusa zamu ma dawo nan ɗin muma. Yanzu haka nazo duba can tsohon gidanmu ne dan asan gyaran da za'ai masa”. Sosai ta kafesa da ido ita da Iyyani. Kafin cikin ƙarfin hali Iffah tai magana. “Amma Yaya su Babiy basa ganin rayuwa zata mana wahala anan sakamakon bamu sababa sam. Sannan ayyukansu dake acan miye makomarsu? Da karatunmu muma?. Abinda ya faru ya riga ya faru, tunda hannayenmu bazasu iya maidosu ba, mi zaisa zukatanmu bazasu cigaba da haƙuri ba. Barowarmu cikin Daular ruman tamkar munji tsorone, ko sake sakin rayuwarmu a hanun waɗanda kansu kawai suka sani.......” “Tsoro halak ne Iffah. Bama muba mafi yawan masu yara mata sunata barin daular ruman a yanzu domin tseratar da ƴaƴansu daga auren jeka nayika. Karatun ƴammata yana neman tsayawa cak, kowace na tsoron fitowa ta zama nama a hanun hadiman daular ruman. a yanda lissafin yake a yanzu an rasa mata goma sha huɗu fa, a tunaninki kafin ƙarewar wannan shekarar ba'a rasa fin hakaba duk da bawai ya cigaba da auren bane.” Wasu hawayene masu ɗaci da ƙuna suka silalo ma Iffah, tai saurin saka gefen mayafinta ta share tana murmushin takaici. “Niko a ganina gudu bashine mafita ba, muryoyinmu ya kama mu ɗaga wa duniya kowa yasan halin da muke ciki, idan har a ƙasar Ruman babu wani sama da nasa mulkin ai a sauran ƙasashen duniya akwai wanda suka fisa...” “Humm Iffah ke yarinya ce har yanzu.” “Sosai kuwa Hanash. Shiyyasa bata gane komai sai abinda yanzu take zuwa da shi”. “Humm Iyyani kenan”. Iffah ta faɗa a yanayin jin raɗaɗi a maƙoshinta. Su duka kallonta sukai, sai dai ta ɗauke kanta gefe tamkar bata gansu ba. Daga haka babu wanda ya sake cewa komai har tsahon wani lokaci. Iyyani ce ta canja hirar da wani abu daban har Hanash ya kammala. Tare da shi suka fita wajen duba tsohon gidan da kakaninsu da suka haifi Babiy ne suka rayu a ciki, dan sudai tunda suka taso a cikin birinin daular ruman suka san kansu duk da a ɗan gefen gari suke acan ɗin ma. Sai dai su shigo cikin ƙauyen Jumna a matsayin duba kakannin nasu. zuwa yanzu su duk sun rasu, shiyyasa gidan ya kasance babu kowa. Duk ma ya rusa ya fita hayyacinsa dan ginine na jar laka tamkar yanda duka gidajen ƙauyen suke. Sun ɗan jima acan suka dawo, sun iske kaka ya dawo shima daga fitar da yay tun ta safe gona ɗebo sassaƙe-sassaƙen magunguna. Ƙara zaman tattaunawa sukayi iya su uku, ita dai Iffah bata cewa komai. Daga ƙarshe ma tashi tai ta shige ɗakin kwananta. Bata sake fitowa ba sai da kaka ya neme ta. Sassaƙe-Sassaƙen magungunan daya ɗibo ɗazun ne a gabansa, kowanne ya ɗauresa daban-daban. Ya turamata babban robar da suke ciki... “Zaki fara amfani da su Iffah, bana son kiyi wasa dan ALLAH. Waɗannan kuma hayaƙine, a kowacce duhun magriba ki tabbatar kinyi turarensu, wannan kuma a ruwan wanka ne, da kin idar da sallar asuba ki zubasu cikin ruwa kaɗan ki cire kayanki ki tabbatar duk jikinki ya samu”. “Tofa kaka wannan ɗin kuma duk na miye?”. Iffah ta tambaya cikin nuna mamaki. Idanu ya tsiramata na kusan mintuna uku tamkar mai nazari, sai kuma ya ɗauke kansa da wani yanayi mai wahalar fassara. “Faruwar ƙaddararmu bashi ke nuna baza'a sake jarabtarmu ba. Idan jiya ta shuɗe da ɗaci zata iya yuwuwa yau ɗinmu da dariya zata kasance, sai dai sanin mike a gobenmu al'amarine mai girman gaske, damin gaibunmu ce ita ALLAH ne kaɗai masanin mi zaizo.” Kallon juna sukai ita da Hanash, Iffah ta ɗan ɗage kafaɗa cikin yanayin ban fahinta ba, shima sai ya kaɗamata idanu alamar shima hakan take. Atare suka maida dubansu ga kaka. Amma sai ya kauda kansa alamar baya buƙatar kowacce irin tambaya daga garesu. Iffah ta jinjina kai kawai alamar ko'oho. Sai kuma ta miƙe tana mai faɗin, “Ni dama fa na yanke shawarar zanbi Akhi mu koma. Tunda dai naji sauƙi gara naje na koma makaranta anata wuceni a darasi”. Ba karamin waro idanu Hanash yay ba, zaiyi magana kaka ya dakatar da shi ta hanyar yin murmushi da kaɗa kansa. “Ita rayuwa rubutacciya ce tunkan halitta, an rubutatane da alƙalamin da ba'a goge rubutunsa, babu wani hannu daya isa gogeta koda da ƙarfin iko. Dole ne sai anyi hakan, ko muna so ko bama so mashin nan sai ya isa inda aka aikashi. Domin ita *KIBIYAR AJALI! SULKE BAYA TARETA SAI TA GITTA*”. A rikice Hanash ya tari numfashinsa. “Kaka bana gane dunƙulallun zantukan nan naka, ka fito fili dan ALLAH ka sanar mana mi kake son faɗa...” “Hanash! Lokacin faɗar baiyiba ai, nima kurman baƙin kawai na gani, fassarar sai UBANGIJI”. Sosai Hanash ya sake tsare fuskar kaka da idanu, kamar yanda itama Iffah tai tsai tana kallon nasa. Su dukansu sun jima da sanin kaka mutum ne hatsabibi, dan kuwa mahaifinsa gawurtaccen masanine da azamaninsa akan kallesa tamkar matsafi ko wani mai gani har hanji, sai dai kasancewar bai ajiye buzu ya zauna akan iya wannan al'amarin ba yasa ake shakkar faɗa, yana bada taimako na magani akan abubuwa daban-daban musamman harkar aljanu komai ƙarfinsu da shaiɗancinsu. Sannan yana sana'arsa ta saƙa kayan kwalliyar doki. Kaka ya gaji abubuwa da dama a garesa, sai dai shi ya watsar da harkar bada maganin dan shima dai a karan kansa yana ta'allaƙa sanin mahaifin nasa da bokancin, duk da dai bai fito fili ya bayyana hakan ba kuwa, amma rashin maida hankali akan abinda ya shafi hakan zaisa ka zargi ko haka ɗinne. Akwai kayan aiki na mahaifinsa da yawa a killace a wani waje da shi kaɗai ya sani, kuma tun bayan mutuwarsa shi ya tattare su ya killace su............✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_4_* _______________ _*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_ _*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._ _*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._ _*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_. _*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._ _*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._ _*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_ _*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._ _*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ *_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._* ________________ .........Iffah tayi mamaki da kaka ya bari salin alin tabi Hanash washe gari, duk da Iyyani taso borewa ita. Amma wasu lafuza daga cuɗaɗɗun kalamansa ya sata yin shiru ta bisu da addu'a. Kaka yayma Iffah gargaɗi matuƙa akan abubuwan daya bata, ya kuma tabbatar mata ko guda ɗaya taƙiyi zaiji hakan a jikinsa. A hankali ta murza awarwarayen hannunta da shine ya sakamata, ta sake lumshe idanunta da sakin ajiyar zuciya. Haka kawai takejin awarwarayen da girma da kuma banbanci da irin wanda take sakawa a baya domin kwalliya, ko miye dalili oho. Daga Ummu har Babiy a tsorace suke kallon Iffah da Hanash da suka shigo. Hanash ya girgiza musu kansa cikin sauri yana faɗin, “Wlhy ba laifina bane Babiy. Itace ta bore akan saita biyoni, kaka kuma ya bata goyon baya. Dan a cewarsa _(Babu wani nisa dake bada tazarar gujema ƙaddara. A wani ajin jarabawar data biyoka ma gara kai ka tunkareta. Dan ba kowane kogo bane ke zama kogo ga ma'abocin gudun ceton rai)._ Babiy na kasa fassarawa, akoda yaushe cirkuɗaɗɗun kalamai daga bakin Kaka masu tsaurine da wahalar fahimta. Dan ALLAH idan kun sani ku fassara mana”. Maimakon amsa daga Babiy baya sukaga yayi tamkar zai faɗi, sai dai cikin sa'a ya dafe gini tare da dafe kansa alamar hajijiya. Ummu ma ƙasa takai zaune jikinta na rawa, hakan sai ya ƙara firgitasu. Da sauri duk sukai kansu suna mai tambayarsu suna lafiya kuwa?. Da kai kawai suka amsa musu, Babiy harda ƙoƙarin ƙaƙaro murmushi. Cikin son kwantar musu da hankali yake kallonsu. “Kunga karku sakama zukatanku wata damuwa, ba maganar Baba bace ba, kawai dai bana jin daɗine kwana biyun nan dama”. Jimm sukai alamar tunani, sai dai kuma babu damar yin musu ko ƙin aminta da cewar tasa. Hanash ya taimaka masa suka koma cikin runfa, Iffah kuma tana riƙe da Ummu.. ★★★ Washe gari batare da sun sani ba Babiy yay sammakon yin tafiya zuwa ƙauyen Jumna. Ya samu tarba daga surukan nasa ko ta girmamawa.... Ƙyaƙyƙyawan tsohon da Tattarowar fatarsa ta tsufa bai hana bayyanar ƙyawun cikar halittarsa ba ya sake kallon dattijon gabansa a karo na babu adadadi. Murmushi ya saki a karon farko, cikin karyar da kai da ƙanƙan da idanu ya kai hannu bisa kafaɗar dattijon. Numfashi yaja kakkaura da juyowa alamar dawowa hayyaci. Ya maida kansa ƙasa ya sunkiyar saboda girmamawa ta surukuta dake a tsakaninsu na tsahon shekaru. “Humm Muhammadu Zayyanu!”. Tsohon ya kira sunan tamkar mai sake bita a ranar da aka raɗa ga mai shi. Ɗago idanu ya sakeyi a karo na biyu sai kuma ya risinar tare da amsawa da “Na'am Baba”. “Tun isowarka magana nake gani shimfiɗe a fuskarka amma bakinka ya kasa furtawa, ko wani abu ya sami Hanash da ƴar uwarsa ne a hanyarsu ta komawa gida jiya?”. “A'a baba ko ɗaya, lafiya lau sukaje cikin ƙoshin lafiya kuma, sai dai.....” Sai kuma yay shiru ya kasa ƙarasawa. Kaka dake kallonsa yay ɗan murmushi, “Sai dai baku so komawar Iffah ba ko?”. “Hakane baba. Domin kuwa babu abinda ya canja a daular Ruman, muna jin tsoron rasata itama kamar ƴan uwanta, duk da bamu da tabbacin zasu sake waiwayrnmu, sai dai kalamanka sun sakamu a ruɗani har muka kasa rumtse idanu a daren jiya domin yin barc......” “Hana ido barci bashi ke nufin damar iya sauya abinda bakai ka rubuta ba. Muhammadu Zayyanu! Da ace ƙaddararmu a hannayenmu take da kaf mutane bazasu zana zaman duniya ba a littafinsu musamman idan sun san koda daɗin busawar iskar dake cikin aljanna ce. Karka damu kanka da sanin sirrin cikin dutsen da ko'a kallo abin firgitarwa ne. Mumini yakan kasance mai azumtar yini daga UBANGIJI, ya kuma sallaci duhun dare daga UBANGIJI domin yaye damuwa ko samuwar nutsuwa a duniyarsa. Gaibu daga ALLAH take, zahirin da yaso mu sani kawai yake iya nuna mana ta isharar rayuwa ko canjawar tunanin zuciyo yi”. Nannauyan numfashi yaja ya fesar tare da jinjina kai, bawai kwanciyar hankalin da yazo nema ya samu ba, sai dai rashin zaɓi ko bakin zaren kamawa ya sashi fahimtar tsohon na masa nuni da shiru ne kawai a zubama sarautar ALLAH ido dan shine kawai gagara misali..... _________________ ★Kwanaki biyu kenan da dawowar Iffah gida, inda dawowar tata ta zame mata tamkar wani famin ciwo a jikinta. Dan a kullum takanyi hawaye sama da sau babu adadi akan rashin ƴan uwanta guda biyu. Komai ta kalla nasu yakan dawo mata da jiyansune mai cike da farin ciki da babu tunanin yankewa. Duk halin da take a ciki Ummu da Babiy na hankalce da ita, tausayi take basu matuƙa, wani lokacin Ummu har hawaye takan share itama. Yau ma tamkar kullum tun bayan dawowarta tai shirin makaranta ta fice badan hankalin su Ummu ya kwanta ba. Kawai dai dan ta dagene akan komawar. Sun bartane ko komawar zaisa ta sake samun nutsuwa da farin cikin da ko'a fuskarta yanzu baka hangosa. Sanye take cikin skirt golden yellow da t-shirt fara da suka kasance Uniform ɗinsu, sai hijjab fari ƙarami shima ta ɗora niƙab ta yanda ƙwayar idanunta kawai ake iya gani. Bayanta goye da school bag. A nutse take tafiya kanta a ƙasa tamkar bata son taka ƙasar har ta iso bakin titi, tsayuwar da batafi ta mintuna uku ba ta samu abin hawa kamar sauran ɗalibai daketa ɓillowa a kowane kusurwa. Makarantarsu babbar makarantace mai ɗauke da ɗalibai masu hazaƙa, domin kuwa an tattarosu ne daga mabanbanta makarantu aka kawo nan saboda hazaƙarsu. Kowa bata kulaba ta shige aji tai zamanta, saɓanin da da kowa yasan Iffah mai tsiwa da surutu, gata ba'a kadata a himma. Kauɗinta yasa mafi yawan malamai saninta ga kuma ƙoƙari. Amma tunda ta dawo yanzu ta canjama kowa, magana ma saita zo har a tashi batai da wani ba. Kamar yanda malaman sukai mata uziri haka ɗaliban ma sukai mata, dan kowa yasan tana cikin yanayin da uzirin kawai tafi buƙata. Duk wanda ya shigo yakan miƙa mata hannu su gaisa, itama babu musu take miƙawa tare da amsa sallamar da sukai mata. A haka har duk ɗaliban ajin suka kammala shigowa malamin farko ya shigo musu. Da farko ta nutsu wajen fara fahimtar darasin da yake musu, a hankali kuma tunaninta ya fara janyewa zuwa ga abinda taketa faman shiryawa da zuciyarta a kwanakin nan har malamin ya kammala ya fita babu abinda ta ɗauka. Haka na bayansa suka cigaba da shigowa basu darasi daban-daban, wani hankalinta na kai wani harya fita babu abinda zatace ta saurara. Ana tashi tana a ɗalibai sahun farko da suka fara fitowa, jitai kawai tana sha'awar yin tattaki da ƙafafunta yau, dan haka bata tsaya neman abun hawa ba ta miƙo titi da ƙafa ta fara tafiya kamar wasu tsirarun ɗalibai irinta da gidajensu ke kusa da makarantar. Tafiya tayi mai nisa sosai batare da nuna alamun gajiyawa ba, harta kusa isowa roundabout ɗin daya raba hanyar gidansu da ainahin titin hanyar masarauta daular ruman. Daga roundabout ɗin ana iya hango ƙaton tambarin ƙosashen zaki da akayisa da gold na tambarin Masarauta. Iffah taja wani kakkauran tsaki da ɗauke kanta zuciyarta na mata zafi. Harta kusa tsallakawa ta hango wata tsohuwa dake riƙe da wani yaro da Uniform a jikinsa da alama titin take so su tsallaka amma sunata inda-inda. Karan farko murmushi ya suɓuce mata ganin yanda yaron ke jan hanun tsohuwar sai sun tafi kamar zasu tsallaka saita fisgo yaron su dawo baya tana masifa. Sallama tai musu, tsohuwar ta amsa mata. Ta gaisheta da girmamawa tare da faɗin, “Ammi kuna so ku tsalla ne?”. Amsawa tsohuwar tai da “Eh Ibnati ”. Iffah ta sake murmusawa daga cikin niƙab ɗinta, kafin takai hannu ta riƙo na tsohuwar dake riƙe da yaron ita kuma. Suna gab da kaiwa tsakkiya yaron ya fisge hanunsa ya koma baya da gudu yana faɗin yabar abunsa a baya. Tsohuwar zata fisge itama tana masifa da kiran yaron ya dawo Iffah ta riƙeta gam suka karasa tsallakawa. “Ammi yi haƙuri barsa naje zan sake tsallako miki da shi. Rufe bakin Iffah yay dai-dai da taka wani bahagon birkin daya bada sautin ƙuuuuuu!!!. Sai sautin fitar ƙara mai razanarwa ta biyo bayansa. Wani irin zabura Iffah tai na juyowa dan ƙarar har tsakkiyar kanta ta jita. Ai batama san sanda ta yaye niƙab ɗin fuskarta ba da waro manyan ƙyawawan idanunta waje gaba ɗaya ba tana mai ambaton sunan ALLAH ganin yaron nan tsaye cak a tsakkiyar titi hancin wata mota gab da shi allamar kaɗan ya hana ayi ɗanyen aiki. Kusan a tare suka isa kansa ita da tsohuwar data fashe da kuka da ƙwala kiran sunan yaron a matuƙar firgice. Iffah da jikinta ke ɓari ta riƙo yaron jikinta tana duddubashi da sauke ajiyar zuciya a jajjere, ganin babu ko ƙwarzane a jikin nasa. Saurin sakin yaron tai ga tsohuwar tasha gaban motar ranta a ɓace ganin mai motar ko fitowa baiyiba ya ɗan leƙone kawai, ganin baima yaron komaiba ya maida kansa yanama ƙoƙarin barin wajen. A fusace ta buɗe murfin, ba saurayin daya kasance drivern motar ba hatta wanda ke gefensa hankalinsa akan lap-top dake saman cinyarsa sai da ya ɗago suka zuba mata idanu. Gaba ɗayansu ta haɗa ta dallama harara da manyan idanunta masu matuƙar haske tamkar madara. “Kai malam baka san darajar mutane bane?....” Zazzaƙar muryarta mai taushi da nutsuwa a cikinta ta daki kunnuwansu cikin faɗa babu ko ɗigon tsoro a tare da ita. Batare data damu da yanda suka zuba mata ido ba ta murguɗa musu bakinta da sake dalla musu harara ta cigaba da masifarta, “Ka kusan bige yaro amma tsabar kanka ba'a daidai yake ba shine koka fito kaga yaya yake ma saboda ku masu kuɗin nan ɗaukar talaka kuke baida banbanci da titin da kuke gurza tayoyin banzayen motocinku da kuka saya da kuɗinmu”. “Kai!”. Drivern ya faɗa da maɗaukakin mamaki Iffah. Harara ta sake dalla masa da zira hannunta ta zare key ɗin motar daya riga ya kashe tun ɓuɗe musu murfin da tayi. “K! K! Dalla bani key kajimun fitsararriyar yarinya kinga mun taɓashi ne?”. “Anƙi a bakun, wlhy duk sai kun fito kun dubashi kun bama kakarsa haƙuri zan baku key ɗin nan, inba hakaba sai dai mu kwana anan.” Hannu saurayin ya kai da nufin warto key ɗin taja baya, sai dai duk da haka saida yaɗan taɓa skirt ɗinta kaɗan. Cikin matsanancin ɓacin rai ta jinjina yatsarta a kan fuskar matashin tamkar zata tsone masa ido. “Idan hanunka ya sake gigin taɓa koda hijjab ɗin jikina ne sai na karyashi, Sannan koda Shahanshan ne yay wannan aikin bai isa barin wajen nan ba balle kai shashasha driver”. “K!!”. Na gefensa ya faɗa cikin matuƙar waro idanu. A karan farko wanda ke hakimce zaune a sit ɗin bayansu lap-top a cinyarsa da tarin takardu a gefe da gefensa ya ɗago ƙyawawan idanunsa dake tattare da matsananciyar gajiya da ƙosawa yana yamutsa fuska. Baya ganin yarinyar, sai dai duk abinda take faɗa raɗam a kunensa zazzaƙar muryarta ke sauka. Baiko kalla yaran nasa ba ya sauke Lap-top ɗin dake cinyar tasa tare da kai hannu ya buɗe murfin. A tare suka zabura, sai dai kafin suyi wani yunƙuri harya fita a motar. Dolo suka fito suma da sauri...........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_5_* _________________ _*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_ _*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._ _*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._ _*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_. _*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._ _*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._ _*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_ _*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._ _*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ *_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._* __________________ ........Kama hanun yaron da Iffah tai da nufin subar wajen duk da key ɗin motar mutanen har yanzu na'a hanunta yay dai-dai da isowar wani nutsatstsen taku mai tafiya da sassanyan ƙamshin turare tamkar shi kaɗai iska ke tsintowa tana busawa a hancinan mutane. Kamar wani magic wajen yay tsitt na wasu sakkani, tsirarun mutanen da suka taru a wajen tun furuwar abun duk suka zuba masa idanu. Ita kanta hajiya Iffah mai masifar ƙirjintane yay wata irin harbawa lokacin da mutumin ya sauke nasa lulu idanun cikin tsakkiyar nata. Da ƙyar ta iya fisgar su daga cikin nasa tana ɗan murguɗa baki da sauke niƙaf ɗinta cike da dakiya. Idanun nasa ya janye daga kanta shima da matsawa gaban yaron ya kai tsigunne dai-dai tsayinsa dan ya fara ɗauka yarinyar nan aljanace ma dai kawai. Cikin sassanyar muryarsa mai zurfi da nutsuwa ya motsa lips ɗinsa kaɗan tamkar an fisgo maganar. “Kana lafiya?”. Kai yaron ya gyaɗa masa. Ya ɗan ɗage gira da motsa bakinsa kamar zai taɓe. “Uhhm! minene sunanka?”. “Amjed”. Yaron ya faɗa cike da kwarin gwiwa. A hankali ya sake kaɗa fararen idanunsa tare da jinjina masa👍🏻 ya saki wani sassanyan murmushi a karon farko da jan kumatun yaron. “Oh my Friend! nice name. Kana sona da aboki?”. Da sauri yaron ya jinjina kai yana washe baki. Idanunsa ya ɗan sake fiddowa suka ƙara girma tare da ƙara sakin murmushi. Ya riƙo hannu yaron alamar suyi musabaha. Al'amarin ya birge mutane da yawa, duk da babu wanda yasan wanene shi, amma ko makaho ya kalla wannan mutumi yasan babban mutum ne. Suit ɗin dake jikinsa farare tas ma kawai abin kallone. Balle shi a karan kansa daya kasance ƙyaƙyƙyawan gasken fatarsa da gogewarta har ɗaukar idanun mai kallo take. Ga wani ƙamshi na musamman mai saka nutsuwa ga mai shaƙa, yanayin kamewarsa da cikakkiyar isa irin ta manyan mutane ke ƙara kawata kwarjininsa da cikar kamala ga duk mai kallonsa. A karo na biyu suka sake haɗa ido da Iffah dai-dai ya gama gaida kakar yaron nan da keta faman washe baki da jera masa godiya dan kuɗine dunkulallu sabbi ƙal ya damƙa a hanun Amjed. Harara ta balla masa da janye idanunta da sauri saboda wani abu mai tsananin sanyi taji yana tafiya daga ƙafafunta har saman kanta. Cike da takunsa na nutsuwa da ƙasaita shima ya juya ya bar wajen kai kace akan dole yake taka ƙasar saboda takun zaratan maza masu cikakkiyar isa da lafiya ce tattare da tafiyar tasa. Iffah ta jefama ɗaya daga cikin samarin nan biyu key ɗin motar, dan ɗayan ya tafi da hanzari ya buɗema ogansu ne. Dai-dai zai shiga ta ballama wanda ta jefama key ɗin harara da faɗin, “Daga yau ko daga nesa kuka hangoni to ku canja hanya koda a jirgi kuke kuwa”. Shigar maganar tata a cikin kunensa dai-dai zai shiga motar da aka buɗe masa ya ɗan ɗago idonsa, sai dai wadda ya ɗago da nufin kallar da mamakinta ke cin ransa tuni ta nufi barin wajen tamkar ba ita ta haɗa dabar wajen ba... Suna ƙoƙarin shan shataletalen titin idanunsa ya sake sauka a kanta ta miƙe titi tana tafiyarta a nutse, sai dai fuskarta a rufe take da niƙab data saki tun bayan haɗa idonsu na farko.... 🤔Wannan ƴa ta Babiy wataran sai ta saka an mata dukan sakwara a titi in har bata canja hali ba😬🚴🏼. ★★......★ “Badai a ƙasa kika tahoba auta? Na ganki a gajiye tamkar an koroki”. Zubewa tai a taburmar da Ummu ke zaune, tare da ɗora kanta a cinyarta tana ƙara narke fuska. “ALLAH a ƙasa na taho Ummu. Haka kawai naji ina son na taho a ƙafan”. “Ai gashi nan duk kin gajiyar da kanki, dama keba wata isashshiyar lafiya ba. Tashi kiɗan watsa ruwa dan sai warin rana kikeyi”. “Kai Ummu warin rana fa?”. Tai maganar a shagwaɓe da kamo rigarta ta kai hancinta. Miƙewa tai tana tura baki gaba da faɗin, “ALLAH Ummu kinso dai yarfanine amma ƙamshin ma turare nakeyi”. Murmushi kawai Ummu tai da girgiza kanta, ita kuma ta shige ɗaki sai faman cika baki take da iska a dole taji haushi..... ★Da daddare suna zaune a tsakar gida cikin hasken farin wata daya raba Hanash na koyama Iffah aikin makaranta. Daga gefensu Ummu da Babiy ne zaune yana cin abinci. Hira suke jefi-jefi akan kayan lambunsa da zai fidda a ƙarshen satin nan ga ƴan kasuwa. Iffah tai karaf jin Babiy yace zuma batayi kirki ba wannan karon bazata wuce tulu biyu ba. “Babiy sai a bar mana mu shanye kawai a gida. Kaga dama Ummu zatamin alkakin saukar islamiyyarmu nan da wata biyu”. Murmushi Babiy yayi, “Zanso haka Ibnati, sai dai bazai yuwuba dan dukanta zan kaita masarauta ne”. Take murmushin fuskar Iffah ya ɗauke baki ɗaya. Kamar zatai magana sai kuma tai shiru ta maida kanta ga aikinta kamar bataji ba. Shima Babiy sai bai sake cewa komai ba akan zumar suka cigaba da maganarsu da Hanash da Ummu dake saka baki jefi-jefi..... Tun wannan magana babu wanda ya sake tada zancen zumar nan. Babiy da Hanash suka duƙufa tattare kayan lambu da za'a fitar. Yayinda Iffah ta cigaba da zuwa makarantarta a zahiri kamar babu wata damuwa tattare da ita. Sai dai kuma a baɗini tun randa akai maganar kai zuma daular ruman zuciyarta sam bata huta ba. A duk motsinta cikin ƙullawa da kwancewa take game da babban burinta na ɗaukar fansa. Wanda tasan bata da wata hanyar yin hakan sai ta wannan zuma da Babiy ke kaiwa masarauta. Kuma tasha jin cewa Tajwar ne ke shanta kawai. Har ana saura kwana biyu bata samu wata mafitaba akan ƙudirinta, dan haka tana zuwa makaranta taja wata ƙawarta da kafin yanzu da ta canja suke sabgarsu da rashinji tare gefe. Ikram da taji farin cikin ƙawarta ta fara dawowa yanda take babu musu ta bita suka koma can ƙarƙashin wata bishiya suka zauna. “Ko kefa Iffah, ALLAH bana jin daɗin yanda kike shareni yanzu sam. Dan ALLAH ki manta da komai mu cigaba da yima su Akia Arfa addu'a”. “Humm”. kawai Iffah tace da ɗan laɓe fuska. “Kinga ni ba wannan yasa na kiraki ba, tambayarki nake so nayi?”. “To ALLAH yasa na sani”. Cewar Ikram tana gyara zama. “Kinma sani, kwanaki bakin bani labarin sister ɗin mamanku tasha zuma taita ciwon ciki ba, kafin aje asibiti har hanjinta ya kakkatse?”. “Yes anyi haka, bayan kwana huɗu ma ta rasu ai. Sai daga baya aka gane ashe saurayintane ya zuba mata wani magani a ciki. Sai dai har yanzu ma ana shari'an, dan a binciken likitoci sudai sunce basuga komai ba, abokinsa kuma da suka ƙulla tare ne ya tona masa asiri, ya kuma rantse sun zuba ɗin dan tare suka sayo maganin”. Iffah dake saurarenta tace, “Anya kuwa ba abokin na masa sharri bane?”. “To mudai bamu san dai-daiba sai ALLAH. Grand mother ɗinmu ma ita tace dan ALLAH abar shari'ar tunda UBANGIJI mafi sani ne. Idan anje garesa shi ya rarrabe ƙarya da gaskiya”. “Uhm gaskiya kam tayi magana mai ƙyau. To amma ni abinda ya bani mamaki, shiko wannan wane kalar maganine haka da har za'ace likitoci sun kasa ganewa, bayan kuma gashi sunce ya kakkatsa mata hanjinta da kansu.” “K nifa abinda na fahimta kamar an sayesu ne likitocin, kin sanfa ɗan manyan mutanene yaron. Amma abokin nasa ya faɗi sunan maganin sai dai na manta”. “Komaima zai iya faruwa indai shegun manyan ƙasar nannne, kansu kawai suka sani azzalumai. Amma ina son nasan sunan maganin dan ina son nai bincike a kansa ma ni wlhy.” “Kedai kawai wani abun adai rufesa kawai. Uhm kina nan da shegen son bincike-binciken nan naki, anya Iffah idan ALLAH ya cika miki burinki na zama ƴar jarida bazaki addabemuba? Dan na kula har hurumin aikin jami'an tsaro zaki dinga shiga tsabar bin kwaf-kwaf ɗinki”. “Ƴar sa ido naji, nidai kafin a tashi ki tuno sunan maganin inba hakaba zanta addabarkine”. Ikram tai dariya tana miƙewa. “Indai wannan ne zanyi ƙoƙari. Maganin ma fa ba wani na kirki bane ba ance ana zubama ƙananun ƙwari ne dakan damu mutane a cikin gida a ruwa haka ko abinci, dan basajin warinsa sam ko ami aka zuba sai kiga sunsha ruwa da shi ko abinci.” “To kinga koda ba bincikeba ai zai mana amfani, dama mu da muke cikin lambu kullum cikin ganin macizai dama halittu masu cutarwa iri-iri dake iya zama a cikin gida haka.” “Eh gaskiya kuma hakane, zai ko taimaka muku insha ALLAHU”. Kafin a tashi kuwa Ikram ta cika alƙawarin samowa Iffah sunan magani. Takoyi farin ciki har haƙwaranta na bayyana wajen murmushi irin wanda ta jima batayiba a rayuwarta. Iya kuɗin motarta ne kawai a jikinta. Dan haka ta gama tsara ƙaryar da zatai ta samu kuɗin sayen maganin idan ta koma gida. Koda ta koma gida tun kafin takai zaune ta sanarma Ummu ai an basu wani Assignment mai wahalar gaske. Gashi bata da littafin dazai taimaka mata tayi har sai ta saya. Ganin yanda tai maganar a serious yasa Ummu yimata murmushin kwantar da hankali. “Karki damu in har ana saidawa anjima sai Hanash ya fita ya saya miki kema, ko kuma ki bincika a kayan karatun su Arfa ƙila ki samu ai”. “Ummu basu dashi sam, dan kwanaki ma da malaminmu yay maganarsa sannan suna nan ai. Kinga da suna dashi ai da sun bani”. “Uhm hakane kuma kam. To ki bari Hanash ɗin ya dawo sai ya dubo miki”. “Ummu ni kawai ki bani yanzu da nayi wanka sai naje da kaina na dubo. Ƙilama daga nan na ƙara ilimi”. “Kai Iffah kin cika fitina, kin dai san ba son yawan fitarnan taki muke ba ai”. “Na sani Ummu, insha ALLAHU babu abinda zai faru addu'arku na biye dani, kuma ina suturce jikina idan zan fita”. Badan hankalin Ummu ya kwanta ba ta yarda tabar Iffah ta fita. dan ta dage akan gobe ake buƙatar sukai Assignment ɗin, idan tace zata jira sai Hanash ya dawo dare zaiyi tunta sunje babbar kasuwar cinikayyar ƙarshen watane ta daular ruman kai kayan lambu. Kamar kullum tai shirinta tsaf tare da rufe duk jikinta sai idanunta kawai da ake gani. Sosai ash color na abayar jikin nata mai adon duwatsu blue masu sheƙi sukai mata ƙyau duk da ba'a iya ganin fuskarta. Cikin nutsuwarta take takunta tamkar wata tarwaɗa. Dan Iffah tun tana yarinya irin yaran nanne masu shegen iyayi da kauɗi. Tun a shekarun baya mutane kance za'ai kallon ƴammata a wajen nan, dan tafi yayunta son kyale-ƙyale da tsantseni irin na ƴan gayun mata masu ji da kansu. Da ƙafa tazo har titi duk da akwai ɗan tafiya a tsakaninsu. Ta tare abin hawa tare da sanar masa inda zai kaita. A ƙofar katon kantin da ake saida duk wani nau'in magani daya shafi gona dana kauda mugayen halittu masu cutarwa ga mutane dakan shiga cikin gida ya sauketa. Ta biyashi kuɗinsa sannan ta shige. Kanta tsaye ta miƙa takardar data riga ta rubuta sunan maganin dan karta manta. Aka faɗa mata kuɗin ta biya suka bata. Wani irin farin ciki takeji a ranta, tunin karta koma gida babu littafi ta zama abar tuhuma ya sata cema mai abin hawan data hawo ya kaita babban shagon littatafai. Koda suka isa cewa tai ya jirata yanzu zata fito su wuce. Gargaɗi ya mata akan kuɗintafa ya ƙaru, tace babu damuwa tana shigewa. Ganin babu yawan mutane a shagon duk da ƙatone sosai ba kuma wajen da za'ai hayaniyar da zaka san adadin mutanen wajen bane yasata ɗage niƙab ɗinta yanda zataga komai da ƙyau. Kowanne littatafai da sashensu a rubuce kuma yanda bazakasha wahalar nema ba, maimakon ta nufi inda zataga irin nata kai tsaye saita fara zagaye. Sai da ta gama kewaye-kewayenta tamkar ta manta da wanda ta ajiye a waje kafin ta tsaida hankalinta ga inda zataga littafin daya dace ta ɗauka. Surutun yara takeji kaɗan-kaɗan ta bayan inda take, ta ɗan dudduba taga babu ta inda zata leƙasu sai ta haƙura cikin taɓe baki takai hannu kan wani littafi zata ɗauka. Daga can ɓangaren ma dai-dai an kai hannu akan littafin za'a ɗauka dan duk kanta ɗaya ce, littatafan ne kawai suka rufe wanda ke can baya ganin na nan. Iffah taja, daga can ma aka ja, jin za'a fisge saboda an fita ƙarfi dama tsaho dan ita harda su ɗiɗɗishe saita fisga itama a ɗan fusace saboda gani take wani keson raina mata hankali. Ta cikin ɗan space ɗin data cire littafin ita da shi suka zubama juna idanu, haka kawai taji tsigar jikinta ta tashi duk da ita bama wani ganesa tai da ƙyau ba saboda space ɗin bawai ya buɗe da ƙyau bane. Kamilalliyar fuskarsa da dama babu wani walwala a cikinta ya ƙara tsukewa dan shiko sarai ya ganeta...........✍ ★ Shin wanene wai wannan dake neman zamema Iffah ɗan kaɗafi?. ★To wai mima zatayi da maganin data saya ne?. ★ Ko Iffah zataci nasarar cika ƙudirinta?. ★Idan taci nasarar minene zai biyo baya?. ★Mike kashe matan Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed ne?. ★Shi kansa Tajwar Eshaan ɗin wanene shi?. ★Yaya yake? Taya zamu san ainahinsa?. *_Duka amsoshin nan na'a cikin gundarin labarin littafin DAUƊAR GORA. Masu iya magana kance (CIKI KA SHATA). To waima miye ma'anar kalmar Dauɗar gora ciki ka shatan ne?🤗. Kumuje zuwa kudai, karku bari a baku labari masoya🤸🏼, dan cakwakiya iya cakwakiya. Kundai san minene gidan sarauta, balle irin wannan na DAULAR RUMAN da Tajwar ɗinta ke amsa suna Shahan-shan. Ma'ana (King of Kings🤴🏻). Bafa cakwakiyar kawai bace, akwai tsumammiyar soyayya mai fasa zuciya😋._* Dawa?. A ina?. Taya?. _Duk amsar na cikin *DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA🤗* dake a ɗaya daga cikin littatafai biyar na *ZAFAFANKU* abin alfaharinku. Kundai sansu kun san aikinsu babu wasa babu jan rai a cikinsa balle shiririta. Zamu gamsar da ku da salon labaranmu a wannan karon fiye dana baya insha ALLAHU. Kudai kawai ku kasance da zafafan naku biyar zakuce nina faɗa muku😋😁._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22799643131 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_6_* ________________ _*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_ _*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._ _*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._ _*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_. _*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za'a kira fari a kowace irin duniya._ _*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa'a koda a cikin dubun da sukafi dubu._ _*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_ _*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._ _*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._ *_Mai azama shi za'a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._* ___________________ ........Baki ta murguɗa da juya idanunta farare tas tamkar madara cikin nasa da ya kafeta da su. “Inma kai mayene to wlhy bazan ciyu ba, Babiy kullum addu'a yake min shi da Ummu”. Tana gama faɗa tabar wajen. Yaransa na waccan ranar ne dai yau ma a tare da shi. Kuma suma sarai kalaman Iffah da bazasu manta muryarta da wuri ba ta shiga cikin kunnuwansu. Dama sune suke dubama yaran dake tare da su books ɗin, shi ko yana biye da su ne kawai da binsu da idanu. Ɗaya daga cikin yaranne ya nuna littafin da Iffah ta ɗauka, su kuma kasancewar suna ɗakkoma sauranne sai shi da kansa yay yunƙurin ɗakkowa kafin su suyi hakan. Yunƙurin zagayowa wajen Iffah ɗaya daga cikin yaransa yayi, dan yay alƙawarin yau sai ya daddala mata mari, amma sai ya dakatar da shi ta hanyar yima ɗayan alamar ya tsayar da shi da ido. Da sauri wancan da shima yake jin kamar suje su haɗu su faffasa mata baki ya kira sunan wancan. “Azaan!”. Cak ya tsaya tare da rumtse ido da cije baki dan yasan dai ogane zaisa Fakhir ɗin ya dakatar da shi. Gashi harya hango Iffah dake gaban mai biyan kuɗi. Dole ya haƙura badan yaso ba, amma yaci alwashin duk randa suka sake haɗuwa da yarinyar can babu oga sai ya mata karyawar gasashshiyar masara danta tabbatar itace zata gujema haɗuwarsu ba su ba kamar yanda ta faɗa. Iffah dai tuni ta biya kuɗin littafi daya cinye mata duka kuɗinta babu ko na bawa mai Mototaxi (napep). Sai mita take a ranta Littafin yayi tsada, koda ta fito ta iske mai Mototaxi ya cika yayi taf. Tana isowa inda yake hannu kawai ya miƙa mata alamar ta bashi kuɗinsa ya wuce. Fuska ta ƙyaɓe ta cikin niƙab ɗinta tana wani kif-kif da idanunta da kawai yake gani. “Oh oh kaiko duk daɗin asara ai ta jira samu ko? Idan mukaje inda zani nace maka bazan biyaka bane?”. A fusace yana mai dalla mata harara yace, “Na fasa kaiki, dalla malama bani kuɗina kije ki hau wata. Kuma har na zaman danai anan sai kin haɗamun”. “Lallai sannu shugaban ɓarayin Ruman. Saboda Babiy yamun baki ko? Idan kaga zaka ɗaukeni muje na baka kuɗinka ka daukeni, in kuma zaka zauna wage baki kana ihu ne na tare wata na hau ka biyoni a baya dan bani da shi anan sai naje gida”. “Baki da hankali”. Mai Mototaxi ya faɗa a matuƙar fusace yana fitowa. Harga ALLAH Iffah ta tsorata, dan tasan wannan mai zubin samudawan ƙarnin farkon fyaɗa daya zai bazar da itane a titin nan sai dai a kaima su Ummu gawarta. Amma tsabar ƙarfin hali sai faman fiki-fiki take da idanu da faɗin, “To sai kayi duk abinda ma zakayi mana”. “Hakama kika ce?”. Ya faɗa yana matsota. Jikinta taja baya tana wani zazzaro masa manyan idanunta masu matuƙar sheƙi tamkar ta tara ruwan hawaye a ciki, “Idan hanunka ya taɓa koda abayar jikina sai na ɓallashi! Idan kuma ka isa ka gwada”. “Kan uban can kayyasa, ke yarinyar nan kin san wanene ni kuwa? To dan ALLAH gwada ɓallamin hanun nagani”. Ya faɗa yana yo kanta da gaske. Securitys ɗin dake a bakin bookshop ɗinne sukai saurin taresa, dama dai ganinsu yasa Iffah wannan hura hancin, ganin ta samu yanda takeso baki ya ƙara buɗewa ta buɗe baki zata cigaba da tsiwa idanunta suka sauka a kan mutumin nan. Yanayin takunsa na isa da ƙasaita kawai saka rawa a zuciyar Iffah yake, sai dai kasancewarta yarinya mai ƙarfin halin tsiya da rashin son a ga gazawarta yasa baka isa ganin wannan tsoron ba a kan fuskarta. Janye idanunta tayi tamkar bata gansa ba, shima sai ya cigaba da takowa tamkar bai ganta ɗin ba yaransa da tawagar yara kusan goma sha biyar biye da su. Kamar waccan ranar yau ma sanye yake cikin suit da sukai matuƙar fidda ƙyawun halittarsa ta tsayayyen mutum, saɓanin ranar na yau baƙaƙe ne, sai dai sunyi matuƙar dacewa da lallausar farar fatarsa mai matuƙar sheƙi da ɗaukar idon mai kallo. Ga mayataccen ƙamshinsa irin na ranar mai saka zuciyar mai shaƙa raunana da nutsuwa. Harya gotasu zai wuce a binsa sai kuma ya tsaya cak, hannayensa duk biyu ya zuba a aljihun wandonsa tare da juyowa. Ita ya fara kallo, sai kuma ya janye lulu idanunsa masu tabbatar da kwarjininsa da kamewarsa ga duk wanda ya kallesu ya maida kan securitys ɗin nan dake riƙe da mai Mototaxi ɗin har yanzu. Azaan daya fahimci mi ogan nasu ke nufi yay saurin faɗin “ku sakesa” duk da har cikin rai baiso hakan ba. Babu musu suka sakesa, shiko sai huci yake idonsa akan Iffah data juyar da kai gefe irin bata sanma mi'ake ɗin nan ba. Hanunsa ɗaya ya zare daga cikin aljihunsa ya ɗan ɗaga rigar suit ɗin tasa. Kuɗine masu yawa ya zaro ya miƙama mai Mototaxi ɗin. Cikin rawar jiki ya kai rissine kamar gwiwarsa zata taɓa ƙasa ya amsa yana godiya kamar zai haɗiye harshensa. Kansa kawai ya ɗauke zai juya suka sake haɗa ido da Iffah. Baki ta tura gaba tana fiki-fiki da idanu da sake ɗauke kanta... Takaici kamar ya kashe su Azaan. Babu wanda a cikinsu bai harari Iffah ba kafin subi bayan ogansu da tuni yabar wajen. Mai Mototaxi da bakinsa ke washe uwa gonar audiga ya kalla Iffah. “A to hajjaju taho na kaiki koda karshen Daular Ruman ne ma”. Wata banzar harara ta balla masa da jan tsaki tabar wajen. Cike da takunta na nutsuwa ta gitta motarsu dake ƙoƙarin barin wajen. Azzan yay ƙaramar ƙwafa, a ransa yana raya shine zai zama sanadin nakasa yarinyar nan kuwa wataran. Mai gayya mai aiki kam da gaba ɗaya zuciyarsa ta gama tabbatar masa yarinyar nan aljanar ce idanunsa ya lumshe a hankali yana mai ƙara gyara zamansa na ƙasaita tamkar ba'a mota yake ba.... Tunda ta samu wata Mototaxi ɗin ta shiga zuciyarta ta tafi tunani. A karan farko take tambayar kanta waye wai wannan mutumin a garin nan?, da ganinsa dai kasan ɗan masu farcen susu ne ko shi a karan kansa ne mai farcen susar. A ƙasan zuciyarta taji tana buƙatar sanin shi ɗin wanene badan wani abu nasa ya birgeta ba. Hasalima haka kawai haushinsa takeji tun akan bige yaron nan da suka kusa yi a waccan ranar da ƙoƙarin guduwa da sukai. Ko kuma ma dai aljanin ne?, dan inba aljani ba taya zata dinga ganinsa duk inda taje gashi har karo biyu.. Tasha ji a bakin mutane ana faɗin ita ɗin ƙyaƙyaƙyawa ce, tafi kowa ƙyau a gidansu, amma ƙyawun wannan bawa da dirarriyar halittar jiki data fuska mai cike da kwantaccen gashi tamkar shiya zaɓama kansa komai sai dai aljanin kam..... Isowarsu anguwarsu ya sata ture tunanin ta nunama mai Mototaxi inda zasu ƙarasa ta amso masa kuɗinsa. Cikin sa'a suna isa ƙofar gidansu sai ga Babiy da Hanash suma an saukesu da alama yanzun ne suke dawowa. Su suka biya mai Mototaxi ɗin kafin su shige cikin gidan bakinta washe tana jera musu sannu da zuwa... Labarin alkairin da aka samu na kayan da suka kai kasuwa su Babiy ke basu ita da Ummu, amma ita rabin hankalinta naga abinda take yunƙurin yine kawai. Ta matuƙar ƙagara ai kiran sallar magrib su Babiy su fice masallaci Ummu ta shiga ɗaki. Ana kwaɗa kiran salla kuwa itace farkon miƙewa yin haramar alwala. Hakan da tai baisa wani yaji daban ba dan kowa yasan Iffah da himmar yin salla. Komi take aka kira salla, ko'a ina take inhar wajen zaiyi ibada zata ajiye abinda takeyi kuwa tayi sallar. Wannan halin nata na ƙara sakama iyayenta da ƴan uwanta sonta, dan tunsu Arfa na raye ma sukansu Ummu takan zaburar dasu akan halin Iffah ɗin na kiyaye ibada da ƙoƙarin yinta akan lokaci. Koda ta shiga ɗakin bayan tayi alwala bakin gadonsu takai zaune dan tana fashin salla ne, sai da taji tsakar gidan yayi tsitt sannan ta ɗan leƙo, babu kowa kuwa Ummu ta shige su Hanash sun fita massallaci. Da sanɗa ta fito ledar maganinta na ɗazu da taketa ɓoyo riƙe a hanunta. Wuff ta afka ɗakin Babiy, cikin sa'a bata wani sha wahalar ganin tulunan da aka cika da zuma ba sabbi ƙal. Ta saki murmushi dajin kamar tai ihu dan farin cikin da takeji a zuciyarta. Amma sai ta kanne cikin rawar jiki da ɗan yin leƙe-leƙe irin na mai tsoron a kamasa yana laifi tana ƙoƙarin buɗe kwalbar. A tulun farko ta zuba kusan rabi, sai kuma ta dakata bisa shawarar zuciyarta akan ta zuba duka tunda bata da tabbacin dukansu Tajwar ɗinne zaiyi amfani da su. Ƙaramin sandan data shigo da shi tasa ta motsa da ƙyau har saida ta tabbatar ya gauraye sannan ta sakama ɗaya, tana tsaka da juyawa ta tsinkayo muryar Ummu na kiranta. Ido ta rumtse da sauri tana ambatar sunan ALLAH, da hanzari ta shiga rufe roban sauran maganin saboda jin kamar Ummu na nufi ɗakin, cikin riga ta saƙa maganin da sandar sannan taɗan leƙo. Can ta hango Ummu ta nufi kitchen ɗinsu, aiko tai wuff ta fito ta faɗa ɗakinsu. Ummu data juyo saboda jin kamar motsi ta sake ƙwala mata kira. Yanzu kam amsawa tai da fitowa tana gyara mayafin abayarta. “Yi haƙuri Ummu ina karatune”. “Shine kuma bazaki mun ko gyaran murya ba zaki barni ina wage baki”. “Kiyi haƙuri to Ummuna”. Ummu ta fito daga kitchen ɗin tana gyara mayafin jikinta itama. “Jeki ki cigaba da karatunki dama motsi naji kamar, amma fara duba kosu Hanash sun bar mana ƙofa buɗe ne”. Da to Iffah ta amsa tana nufar hanyar soro da sauke ajiyar zuciya... Tana shiga ɗaki wani uban tsalle tai ta dirga saman gadonsu dan farin ciki. Mulmula take tana dariya irin wadda ta jima batayi ba, wauta da ƙuruciyarta tafi hango mata nasararta na ɗaukar fansar ƴan uwanta fiye da tunanin idan wani abu ya faru Babiy ne na farkon wanda za'a tuhuma kasancewar zumar daga hanunsa ta fito. Haka Iffah ta ƙarasa wannan dare cike da zumiɗin ganin wayewar gari Babiy ya kai zuma masarauta. Bayan ta idar da salla yau ko fama da ita Ummu batai ba akan shirin tafiya makaranta, a da kuwa saita tasota daƙyar kasancewarta mai son barcin safen tsiya da tayi salla take komawa barci. Babiy kansa saida yay mamakin wannan sammakon tashi nata yau, Hanash kam kasa haƙuri yay saida yay magana. Sai cewa tai ai sunada program ne a makaranta yau... Koda taje makaramtar ma dai bawai ta nutsu bane, rabin hankalinta ne kawai ga duk malamin daya kasance da su har aka tashi. ★A ɓangaren Babiy kam duk da tabon da masarauta daular ruman ta bar masa a zuciya bai taɓaji koda wani zai bari ya cutar da su ta hanyarsa ba ko shi ya aikata hakan ta damar dake hanunsa na kai musu zuma. Tsaf yay shirinsa kasancewar yau juma'a ce ya ɗiba tulunan zumar nan guda uku ya nufi daular ruman. Idan yaje ba kaitsaye yake ɗaukar zumar nan ya kai ga Tajwar ba, dan ganin Tajwar kam babban abune da sai wanda ya cika ya tumbatsa keda wannan damar. Akwai wanda keda alhakin amsarta shi ya isar da ita inda ya dace har ta isa ga sashen Tajwar ɗin. Bayan ƴan bincike a kansa na kullum da basa ƙarewa ya shiga daular ruman iya ƙofa ta biyu. Dattijo da kamanni da suturar jikinsa kawai ta isa tabbatar maka da shima wanine ya iso ga Babiy bayan zaman jiran kusan mintuna goma da yayi. Cikin girmamawa Babiy ya gaidashi duk da zasu iya zama kusan sa'anni da shi. Shiko ya amsa yana hura hanci irin na masu dama ta mulki a hannu. Umarni ya bama Babiy akan ya ɗanɗana zumar, Babiy da yasan babu wani abu na razani ko shiga dogon tunani kafin ɗanɗanawar kansa tsaye ya kai hannu ya ɗauka cokali dake bisa tire a hanun hadimin dake biye da dattijon nan. Tunda dama haka ba sabon abu bane garesa duk sanda ya kawo sai ya ɗanɗana ɗin. Tulun farko ya kwancema baki kasancewar a ɗaure bakin yake da ganyen ayaba, yasa cokalin nan ya ɗibo zumar da bismillah ya nufi bakinsa.........✍ *_😬😬😬Iffahhhhhh!!!!🙆🏻._* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +2290165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_7_* .........Haniniya da ƙarar takun sawayen wani farin ingarman doki ta saka Babiy sakin cokalin da yake shirin kaiwa bakinsa ya miƙe domin ceton kansa kamar yanda Dattijo nan da hadiman dake tare da su suma sukai nasu waje. Tuni tulunan zumar uku da Babiy ya kawo sukai nasu gefe suma, gaba ɗaya zumar ta kelaye a wajen. Cikin daka tsawa dattijon nan ke duban hadiman da suka biyo dokin domin kama shi... “Wane mara hankalinne yay sakacin daya kunce?”. Su dukansu jikunnansu rawa yake, cikin ƙarfin hali shugaban hadiman dake kula da barga ya zube ƙasa yana mai girgiza kansa. “ALLAH ya ƙara maka tsahon rai an gama masa wankane za'a maidashi na rantse maka”. Dattijon ya cije baki mai nuna alamar takaici, “Na baku mintuna goma kacal ku madashi shashashu kawai”. Miƙewa hadimin dattijon yayi cike da girmamwa dan dama sauran sunata ƙoƙarin ganin sun kama dokin ne, bama su kaɗai ba hadiman da yawa sun ƙaru saboda bahagon dokine da babu ma iya controling nashi sai Tajwar Eshaan. Horarran doki ne daga horonsa, da abinsa ya dawo ƙasar ruman, dokin yafi kowanne doki tsananin ƙarfi a masarautar. Shiyyasa idan har sukai sakaci ya ɓalle kowa sai ya jigata kafin a kamashi da ƙyar, kafinma kamashin sai an samu wanda sukaji raunika da yawa. Akwai randa irin haka ta taɓa faruwa baƙaramin jigata mutane yay ba harda masu karaya a hadimai, kuma duk iya wahala da jigata babu wanda ya iya kama dokin har duhun magriba yayi dan da yamma al'amarin ya faru. Kowa yayi laushi an rasa in za'a kama sai ga Tajwar Eshaan ya fito sallar magrib, abu mafi ban mamaki daya saka masarautar yin shiru na sakanni uku kiran sunan dokin kawai yay sai gashi gabansa, ya girgiza jikinsa tare da yin haniniya sannan ya koma kan ƙafafunsa ya tsaya cak tamkar bashiketa jigata mutane da hargitsa wajen ba. Wannan abun mamaki ya saka dukan hadiman da suka zube saman gwiyawunsu kawunansu a ƙasa a lokacin kasa haƙuri sai da suka saci kallon dokin dama Tajwar Eshan ɗin da hirami daya yafa a kansa ya rufe rabin fuskarsa..... ★★★★ A ɓangaren Iffah gaba ɗaya idanunta sun kasa barin ƙofa, babban burinta kawai dawowar Babiy taji zuma ta isa hanun Shahanshan. Sai dai shiru kakeji har akai sallar juma'a bai shigoba. Ko abinci babu yanda Ummu batai da ita tai zaman ci ba amma taƙi, Hanash ma sai da ya mata maganar tazo suci kamar yanda sukanyi duk juma'a tunma su Fariha nada rai amma tace batajin yunwa. Ƙyaleta sukai dan sun kasa gane minene ya hanata nutsuwa waje ɗaya. Babiy bai shigo gida ba sai bayan sallar la'asar. Azabure Ummu ta miƙe tana kallonsa. “Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un. Abu Hanash haɗari kayi?”. Kai Babiy ya girgiza mata yana kaiwa zaune da ƙyar. “Ke dai bani ruwa na fara sha”. Kafinma ya rufe baki Iffah da itama jikinta ke rawa ta kawo masa ruwan, dai-dai nan Hanash ya fito daga ɗakinsa cikin shirin fita ƙwallo. Shima a ruɗe yay kan Babiy ɗin yana jera masa tambaya. Babiy ya ajiye kofin ruwan yana mai kallonsu gaba ɗaya. “Kunga ku kwantar da hankalinku babu abinda ya faru daga masarauta ne. Wani bahagon dokine fa ya kunce al'amarin tamkar yaƙi, hatta da zumar dana kai ba'a mora komai a cikinta ba ma”. Ummu da Hanash suka shiga jera salati, yayinda Iffah taji wani ƙududun baƙin ciki ya tokare mata maƙoshi, hakan na nufin bataci nasara ba sai ma Babiy daya dawo da raunika. Jitake kamar taga Tajwar Eshaan gabanta ta shaƙesa da hannayenta har sai ya bar duniya saboda tsabar tsanarsa. Har Hanash ya gama yima Babiy dressing ciwukan batace komai ba, daga ƙarshe ma ɗaki ta shige ta shiga faman kaikawo na tunanin abu na gaba. Dan tayi alƙawarin bazata taɓ haƙuraba sai ta kai *_Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed_* ƙasa zata samu salama game da rasa ƴan uwanta. Sam a wannan dare Iffah bata wani isashen barci ba saboda ƙullawa da kwancewa aka shiri na gaba. Abinda ta gama ƙullama zuciyarta yasata shirin fita a gidan da hantsi da dalilin cewar zataje wajen Ikram duba mamanta bata da lafiya bazata jima ba. Ummu tayi kamar bazata barta ba amma taita mata magiya harta amince da sharaɗin karta jima, kuma dolene ta rufe duk jikinta. Ta yarda da hakan saboda tana son fitar. A gurguje tai shirin fitar, tare da lalubo wayar Arfa a cikin kayansu. Koda ta haɗa batteryn ta kunna tayi sa'a tanada caji, dan haka ta loda number da take buƙatar kira tana mai addu'ar ALLAH yasa akwai kuɗi ma. Addu'ar tata bata amsu ba, dan haka ta tura wayar cikin jikinta bayan ta kashe sannan ta fito tai sallama da Ummu ta fita bayan ta amsa kuɗin taxi. Sai da ta fito daga cikin anguwarsu gaba ɗaya sannan ta tsaya ta sai kati, koda ta loda sai ta sake gwada kiran lambar ɗazun. Cikin sa'a kuwa aka ɗauka, jimm sukai su duka kafin ta katse shirun da sallama. Daga can aka amsa a noƙe alamar rashin sanin dawa ake tare. Fahimtar hakan ta saka Iffah bashi amsa tunkan yay tambayar. “Sir! Kana magana da Fareedah bint Zayy......” “Serious?”. Ya faɗa cikin katseta da alamar zabura tun kan ta ƙarasa faɗa. Baki ta ƙyaɓe a ƙasan zuciya tana jan tsuka, a zahiri kam sai ta saki murmushin da har sautinsa ya kai cikin kunnensa. Cike da sake ƙanƙan da kai tace “Tabbaci Sir. Ina buƙatar muhaɗune yanzu yaya za'ayi?”. “Kai! Iffah! Ke ɗin dai?...” “Bazan samu damarba ko......?” Cikin sauri ya katseta. “No ba nufina kenan ba, kawai na shiga al'ajab ne. Amma bara na ajiye tantamar tawa gefe dai. Inaga zanzo na sameki gida kawai...” “A'a sir”. “Miyasa?”. “Ba buƙatar hakan, mu haɗu kawai”. Jimm yayi na tunani, sai kuma ya sauke numfashi. “Okay! okay inaga bara na tura miki adireshin inda nake a yanzu haka sai mu haɗu nan in ba damuwa ko”. “Ya dai kasance babu abinda zai shafi mutuncina a wajen sir”. “Wannan shike ƙara samun naji ke ta daban ce Iffah”. Baki ta sake ƙyabewa. Amsa garesa kuma tace “humm” kawai. ★ Kallon baki da hankali mai haɗi da tsoro tun daga ƙarƙashin zuciya yake mata tun bayan gama masa dogon jawabin da tayi. Tasan zataga fiye da hakan ga kowa bama shi kawai ba, dan haka bataji komai ba sai ma murmushi data sakar masa. Bata san mi yake tattaunawa da zuciyarsa ba, amma tanaji a ranta yana auna shekarunta da maganganun da kowa zai auna da wautarta ne kawai. Ilai kuwa sai ta tsinkayi muryarsa da irin amsar datai tunanin samu. “Nikam Iffah shekarunki nawa?”. “Ashirin a kwashe biyu sir”. Ta faɗa tamkar bata fahimci alaƙar tambayar tasa ba. Kansa ya jinjina da cije lips nashi, kansa tsaye yace “Nama tunaninki mai kama da mafarki uziri. Amma zan baki shawara data dace da waɗanan shekarun naki na ƙuruciya. Ƙoƙarin ya kamata kiyi wajen cinye jarabawar share fagen shiga jami'a da ke tunkaroki kamar yanda nasan burinki. Tunaninki kuma ya zam tamkar baki taɓa yinsa ba, sannan na kasance na farko kuma na ƙarshe da kika faɗawa. Hakanne zai baki damar cigaba da ƙyaƙyƙyawar rayuwar da kika fara da ke da ahalinki har nima na cigaba da saka rasan samunki matsayin uwar ƴaƴana wata rana dan ALLAH Iffah”. Ya ƙare maganar da haɗe hannaye alamar roƙo.🙏🏻 “Ƙyaƙyƙyawar rayuwa ta daɗe da yankewa a cikin rayuwata data ahalina. kuma irinta nake hangowa da son daƙilewa ga ƴan baya ciki harda ƴaƴan da kaima a karan kanka zaka iya haifa wataran Sir. Sannan wannan tsoron da nake gani yanzu a cikin idanunka shine zai tabbatar da hakan, koda ni bana raye kai zaka rayu ka tuna. Nagode da saurarena da kayi sir”. Da sauri yasha gabanta kasancewar ta riga ta miƙe. Tai takwaf-takwaf da fuska tana mai tsaresa da manyan idanunta da tuni hasken cikinsu ya koma launin ja. “Ki fahimceni Fareedah, koba komai na fiki shekaru, na fiki ilimin sanin rayuwa dama sirrikan dake zagaye da lungu da saƙo na ƙasar Ruman....” “Na sani sir, tabbas na sani shiyyasa ma na fara nemanka. Sai dai nima kayi haƙuri, dan babu shawararka ɗaya data shiga cikin wannan kan nawa, saboda abinda ke cikinsa tamkar kundin littafin da aka rubuta labari daki-daki ne, kaga dole zaizo feji bayan feji. Kuma duk abinda ya shiga ciki bazai taɓa goguwa ba sai ta hanya ɗaya tak! Mutuwa!. Mutuwa ce kawai zata goge wannan yunƙurin insha ALLAH. Na barka lafiya”. Sororo ya bita da kallo harta tare mototaxi ta shiga, ji yay ta ƙara masa girma a ido, girma bana shekaru kawai ba na wata ilhamar kwarjini da cikar mutuntaka. In har yara irinta da ayanzu suka fara rayuwa zasuyi irin wannan tunani akan al'ummarsu mi manya kakaninsa, iyayensa, yayunsa dama sa'aninsa sukeyi ne su? Shin basa ganin abinda take gani ne? Ko kuwa da gaske tsoron data ambata ta gani a cikin idanun nasane a idon kowa?. Kenan hatta da sauran sarakunan ƙasar da mafi yawan cikinsu sun rasa ƴaƴansu suma cikin tsoron suke? Anya maganar mutane ba tabbatacciya bace akan danganta Shahanshan na daular ruman da magajin fir'auna daya shuɗe batare da labarinsa ya gushe ba?. Iffah! Iffah!! Da gasken gaske ke tadabance kamar yanda nasha faɗa a aji aduk sanda kika bada amsar data danganci darasi...... ★★★ Kwanaki uku kenan da Iffah ta tunkari malaminta batare da nasara ko ƙwarin gwiwa daga garesa ba. Sai dai hakan baisa taji ta sare ba ko haƙura da ƙudirinta. Koda ace nata ajalin take tunkara tayi alƙawarin sai tabi kadin jinin ƴan uwanta guda biyu. Koda ace bata da ƙarfin ikon ruguza mulkin sarkin dake kama da mulki irin na fir'auna zata tabbatar sai kuwwar gunjin kukanta ta fita a duniya, koba komai tanada yaƙinin a bayanta zata samu masu share mata hawaye insha ALLAHU. Hanyar da tabi a farko ita kaɗaice hanyar da tasan tanada ita wajen bi ta samu nasara cikin sauƙi. Sai gashi kuma ba'a dace ba. Gashi tabi ta biyu itama, sai dai anƙi buɗemata ƙofar saboda tsoro da ƙarfin tasirin mulkin azzalumin, a yanzu haka tunaninta hanya ta uku koda itama bazata samu nasarar ba. Zata kuma cigaba da bin hanyoyin koda zasu ninka dubu sau dubu har sai ta dace. Nannauyan numfashin data zuƙa ta fesar, tare da gyara kwanciyata ta jawo wayar Arfa da har yanzu bata bari wani a gidansu yasan da tana amfani da ita ba. Ido sosai ta tsurama wayar, tabbas ba gizo bane tarin missed call ne daga malaminta. Taruwarsu da rashin jin sanda suka shigo wayar kuma nada nasaba da kasancewarta a silent. Tayi kamar zata share amma sai ta kasa hakan. Dan a yanzu shine kawai madubin da take kallo matsayin damar dake a hanunta ta isa ga abinda take so da wurwuri. Cikin sa'a tana kokarin kiransa sai ga kiran nasa ya sake shigowa. A dakile ta amsa tare da masa sallama murya a cuɗe. “Kiyi haƙuri”. Kalmar farko data fara fita a bakinsa. Iffah taja numfashi mai nauyi tare da haɗiyewa muƙut. “Sir bakamun laifin komaiba nikam”. Ta faɗa tamkar komai baima faruba. “Humm” ya faɗa shima, sai kuma ya ɗora da faɗin “Ina son mu haɗu”. “Babu dalilin hakan sir”. “Akwai Fareedah, kar kiyi taurin kai”. “Koba komai kai ɗin malamina ne ai, mi zaisa na maka taurin kai?. Iya gaskiyata nake faɗa maka”. “A cikin gaskiyar taki harda haƙura da samun abokina”. Zumbur ta miƙe zaune tamkar wadda aka kwantsamawa a radu a tsakkiyar kunne. “Sirrrrr!.....” “Na amince zan haɗaki da shi”. Ya katseta da sauri. Jitai tamkar ta sandara ihu ko zaifi fahimtar farin cikin dake a tare da ita, amma sai tai ƙoƙarin gimtsewa. “Sir ba dole sai shi kawai bane zaiyi aikin, harma na samu wan....” “Fareedahhh!”. Ya faɗa da wani yanayi a muryarsa. Ajiyar zuciya ta sauke a ƙasan maƙoshi. Sai kuma ta lumshe idanu tamkar tana a gabansa tace, “Shikenan ka turamun adireshi. Sai dai inda bazai taɓa mutuncina ba”. Murmushi yayi mai sauti, tare da faɗa kamar yanda ya saba tun acan baya. “Fareedah ke ta dabance ƙwarai da gaskeeee”. Baki taɗan laɓe batare da tace komai ba ta yanke wayar..........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +2290165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_8_* ..........Zaune takai a kujerar dake duban tasa tana mai kallon agogon hanunanta. Ya saki murmushi cikin kafeta da idanu. “Daga zuwa sai duba agogo?”. “Hakan dolene Sir, domin ko lokacin islamiyya zan cinye anan. Kaga kenan sai da tsantseni”. “Okay”. Ya faɗa yana gyara zamansa. “Ba buƙatar maimaita abinda ya faru baya, na gaba kawai yanzu shine zanyi iya ƙoƙarin ganin na haɗu da abokin nawa koda ta waya ne, kin san aikin nan nasu yana hanasu samun isashen lokaci matuƙa kasancewarsu manya dake tare da babbar kafar yaɗa labarai mai aiki da kamar duniya gaba ɗaya. Ke yanzu a gareki miye shirinki?”. Kafaɗa Iffah ta ɗan ɗage cikin jan iska da hurowa. “Kusan dukan shirina a kammale yake, burina kawai nasamu yin hira da African Aye👁️‍🗨”. “Indai hakane haɗuwa da abokina kawai ya rage mana, fatana dai bayan ni kar wanda yasan wannan hatta a gidanku, inba hakaba zamu iya shiga haɗarin da har burin rayuwarmu ma bazai cikaba bayan wannan. Nikuma zanyi duk yanda zanyi insha ALLAHU wajen hana wannan sirrin fita daga gareni....” “Shi abokinka ɗin fa?”. “Baki da matsala da shi domin shi aikinsa ne”. Kai ta jinjina masa fuskata cike da murmushi. Sai kuma ta rissinar da idanunta alamar jin kunyarsa saboda kallon daya kafeta da shi. Kunyar nada nasaba da tuna yanda ta dinga wancakalar da shi da manufarsa a sanda yake malaminta. Sai gashi shine na farko data fara tunkara da matsalata a yanzu duk da kuwa tana kallonta a kan matsalar data shafi kowa na ƙasar Ruman ne. Sautin murmushinsa ya sakata ɗagowa ta ɗan kallesa, sai kuma ta sake kauda kanta gefe itama tana murmushin. “Hummm!” Ya faɗa yana miƙewa. Itama miƙewar tayi batare data yarda sun sake haɗa ido ba. “Kije gida zamuyi waya”. “Nagode sir, ALLAH ya tsare gabanka da bayanka”. Jin sautin murmushinsa ya tabbatar mata jin daɗinsa, amma sai tai gaba da sassarfa tunkan ya sake cewa komai........ ★__________________★ *_DAULAR RUMAN (MASARAUTA)_* Katafaren ɗaki mai ɗauke da ƙayatattun kayan more rayuwa, kwance take bisa lafiyayyen gado da dukkan nau'in shimfiɗunsa suka kasance na alfarma. Sautin dariyar dake tashi cikin kunnuwanta tamkar mafarki ya sata buɗe idanu, cikin tsumar jiki ta ture lallausan bargon da take ciki, tamkar walƙiya ta dire ƙasan lafiyayyen kafet ɗin dake malale gaban gadon tai kneel down tamkar mai neman gafara, kanta a risine alamar nuna tsantsar girmamawa..... Tamkar shirin film ko labaran almara tsohuwa tukuf sanye cikin jajayen kaya ta bayyana bisa baƙar kujerar ƙarfe mai ɗauke da adon gold a cikin ɗakin. Baƙace matuƙa mai tsananin muni da jajayen idanu, yanda ta zauna ƙafa a harɗe kai ka ɗauka itace Shahanshan ɗin..... “Lafiya da tsahon rai su ƙara kasancewa a rayuwar *_Uwa_* mai share kukan masu kuka”. Hamshaƙiyar matar ta faɗa cikin tsantsar girmamawa ga tsohuwar dake harɗe saman kujerar tata tamkar sarauniyar ingila. Cike da isa da ƙasaita tsohuwar taja wani kakkauran numfashi da sake faɗaɗa girman ƙofofin hancinta ta hanyar hurashi, ƙara harɗe ƙafafunta tai tana mai motsa yatsun hanunta, idanunta jajaye kafe akan matar. Cike da isa da ƙasaita mai ɗauke da rashin daɗin muryarta ta tsufa ta fara magana. “Ta-ƙurya kin kusa cin nasara wajen cika sharaɗi na biyu akan alƙawarinmu. Na tayaki murna, saura sharaɗinki na ƙarshe, mafi wahala a cikinsu”. Ƙasa ta ƙarayi da kanta cike da girmamawa a gareta, da dukkan ƙarfin zuciyarta ta furta, “Kece madubin nasarata Uwa!, duk inda akaga naje da jagorancinki na isa. Yanda na cika na farko shima na biyu zan cika sa, nayi alƙawarin cika na ƙarshe ma fiye da yanda kike tsammani.....” Jajayen idanunta masu kama da garwashin wutar gidan biredi ta ɗago tana kallon ƙyaƙyƙyawar kuma hamshaƙiyar matar dake gurfane a gabanta. Ta ƙyalƙyale da wata dariya mara daɗin saurare ga kunen kowa, sai kuma ta gimtse tamkar ba ita tayi ba tana zaro manyan jajayen idanunta kamar na dodanni. “Ta-ƙurya nasan zaki iya, sai dai akwai wani babban ƙalubale dake tunkaro cikar nasararki ta biyu, kuma gab yake da cimmawa, idan baki gaggauta datsesa ba, zakiyi biyu babu”. A razane ta ɗago tana kallonta cikeda bushewar zuciya, sai kuma ta maida kanta da sauri ta rissinar “A gafarceni Uwa, a kawar da ko miye mai son yima cikar burina kutse. Na rantse da ALLAH daya halicceni, koda cikin yankin ahalina ne bana buƙatar numfashinsa Uwa!!”. Dariya ta sake ƙyalƙyalewa da shi sai kuma ta gimtse fuska. Kanta ta shiga girgiza mata da dukkan isa. “Ta-ƙurya wannan karon akwai banbanci da koyaushe, dama na taɓa faɗa miki bayan cikar nasararki ta farko akwai ƙalubale dana gani akan cikar ta biyu, sai dai ba'a buɗe mun komaiba a wancan lokacin, alamar haka na nuna ƙarfin taurarin mai yunƙurin, amma a daren jiya dana tsananta bincike akan mafarkinki na gano wani yanki da ƙyar. Ƴar shilar suda na ƙoƙarin yin cara irin ta gawurtattun zakaru a kunnen bututu da taimakon wata zuciya mai son kusantar tata.” “A taimakeni a kawar mun dasu gaba ɗayansu Uwa. Ko a bani damar kawar da su da kaina”. “Hhhhhhh!!!! Ƙaddarar ƴar shilar bata mutuwa bace cikin sauƙi. Tana kuma da ƙarfin taurarin da zata iya cin nasarar dusashe naki”. Bugawar da ƙirjinta yayi ta zata zuciyarta ce zata fito ta bakinta dan tsabar razana. Ta kafeta da idanu cikin wani irin yanayi mai wahalar fassara. Sai kuma tai saurin maida kanta ƙasa ta rissinar tana faɗin, “A gafarceni Uwa”. Wani irin kakkauran numfashi mai cike da gargaɗi tsohuwar taja, cike da ƙasaita tana yamutse mummunar fuskarta ta cigaba da faɗin, “Zamu iya samun mafita sai dai akwai ruɗani a cikinta. Har zuwa yanzu kuma ban samu buɗewar ruɗanin ba kai tsaye. Dan haka kina da zaɓi biyu. Kodai ki ƙara yin duk yanda zakiyi igiya ta ƙullu tsakanin Malik-alMuluk da wannan ƴar shila muyi duk yanda zamuyi tazama cikamakin aikinmu na biyu, ko kuma ki barta ta cimma burinta.......” Idanunta da suka kaɗa jajur tai ƙoƙarin ɗagowa, sai dai ta maidasu da sauri zuwa ƙasa. “Uwa amma kin faɗamin na cinye jarabawa ta biyu da zarar ya aura cika makin matansa shine matakan nasarata, yanzu haka akwai su su biyu da suka rage ɗauke da aurensa a kansu, zasu miƙasu garesa a karshen watannin nan kamar yanda na samu tabbaci. Taya zamu shigo da wata bayan aikin ya cika. A yanzu ya rage kawai samun cikar burina na ƙarshe ne a kansa. Miye dalilin shigowar wannan yarinyar abinda bai shafeta ba? Mizai hana ai mata wani hukuncin daya dace da ita?...” Hannu ta ɗaga mata cikin tarar numfashi da ƴar hasala-hasala, da kakkausar murya tana mai nunata da ɗanyatsa “Amma har yanzu ban sanar dake wadda ta dace ba, kuma damun san cutarwace na umarninmu gareki bazamu ce ta shigo ba”. “Hakane Uwa, a gafarce ni. Sai dai Mahaifiyar Zak.......”. Ta faɗa da alamun shiga tashin hankali mai girma, amma kallon da Uwa ta watso amata ya hanata ƙarasawa. Bata tanka mata ba, sai dai yanayinta ya nuna a hasale take, dan cikin kaushin murya da zunzurutun jin zafi ta kaɗa ƙahon hanunta mai kama da kwarkwaron gidan dodon koɗi. A take haske ya gilma, sai ga farar takarda a hanunta. “Ƴar shila burinta shine ɗaukar fansa, domin biyu a cikin masu ɗakin Malik-alMuluk da suka shuɗe jininta ne. Burinta shine bin kadin jininsu ta hanyar bayyanama duniya ko kawar da shi. Bayyanawar tata kafin cikar burinki faɗuwarki ne, a yanzu haka kuma ta haɗu da mai taimaka matan harma sun gama magana”. Sosai zuciyarta ta ƙara harzuƙowa. Amma sai batace komai ba saboda ganin Uwa a hasale take da ita. Cikin yin ƙara ƙasa da kai tace, “Da ace bayan cikar burina ne kauɗi da ƙudirin ɗaukar fansar wannan yarinya ya shigo haske ne ga cikar burina. Dan zata ƙarasamin aikin ƙarshe da zanyi. Amma tunda ta shigo a tsakkiyar labarina dolene ta fuskanci hukuncin daya dace da ita. Idan ita bazata mutun ba shi a kawar min da shi mana Uwa”. “Hakan mai sauƙi ne, sai dai shima babu buƙatar mutuwarsa, dan zai iya mana amfani a gaba. Sannan shi rabata da shi shine mafi ƙololuwar hukuncinsa. Dan haka daga nan zuwa safiyar kowace juma'a ta ƙarshen shekarar nan ki tabbatar an zarga igiya tsakaninta da Malik-alMuluk, a dakatar da kai masa matan da suka rage a kaita garesa bayan tarewa, dan da ita zamu cigaba da amfani har samuwar cikar burinmu ga kowa!!.” Da sauri ta ɗago kai jin muryar nayin nesa da ita, sai dai kafin ta iya furta wani abu Uwa ta ɓace daga ɗakin tamkar guntun girgijen hadari a tsakkiyar fararen gizagizai. Zumbur ta miƙe tana mai dafe kanta dake sara mata, wani irin tuƙuƙi da ƙaiƙayin mai zafafa ruhi zuciyarta ke mata. Sai dai sanin wacece Uwa ya sata jin ɗan sassauci kaɗan, amma ruɗani mai ɗauke da abubuwa masu matuƙar yawan gaske da fassarasu a ɗauka shekara dubu bisa dubu ba'a kammala ba na neman danne wancan ƙwarin gwiwar. Taya ruhin ƴaƴan sarakunan ƙasar Ruman basu bata matsala ba sai ƴar talakawa ƙasƙantattu? Dolene yarinyar nan ta ɗanɗana kuɗarta na hukuncin shiga gonar daba tata ba ƙwarai da gaske, sai tayi wasa da ita a tsakkiyar titi wasa irin na ɓera a hanun mage, dan ko ita Malikat bata isaba..... (Tofa masu karatu, ita kuma wannan wacece ita? Iffah fa ta taro match ɗin da babu players. Kumuje zuwa dai muga yaya wasan zai kaya🚴🏼...) ★__________________★ *_IFFAH_* A ɗan firgice ta buɗe idanunta tare da tura hannu ƙarƙashin filon data tada kai ta sake danne wayar dake faman ɓurari cike da tsoron kar Ummu ta jiyo, dan tasan Babiy da Hanash basa gidan. Ajiyar zuciya ta sauke mai matuƙar ƙarfi da zaro wayar, cikin rawar jiki ta dannata a silent. Tamkar jira kiran ya sake shigowa kuwa. Idanunta masu matuƙar girma da haske ta waro sosai ganin mai kiran, ai batama bari tayi ring na biyu ba taa ɗaga tare da kaiwa kunnenta tana direwa a gadon. “Kina jina?”. Aka faɗa daga can. Kanta ta jinjina masa tamkar tana gabansa dai-dai tana leƙawa tsakar gidansu. Daga can gefen da Babiy ke kiwon tsuntsaye ta hango Ummu, dan haka ta sauke ajiyar numfashi da fara magana cikin raɗa. “Ina jinka Sir! Ta samu ne?”. “Babu lokacin dogon magana Iffah, kiyi ƙoƙari daga nan zuwa awa ɗaya ki sameni, dan kuwa mun tsinta dami a kala Ajmal ya shigo Ruman, kuma a yanzu haka mun gama magana da shi sai dai ban sanar masa ainahin zancen ba, ya kuma buƙaci haɗuwa dake.....” “Ya ALLAH! Alhmdllhi. Naji daɗi matuƙa wlhy Sir. Insha ALLAHU duk yanda zanyi kuwa zan fito ka saurare ni”. “Okay”. Kawai ya faɗa yana mai yanke wayar. Itama shiri ta shiga faman yi a gaggauce, tare da tattare takardun dukkan bayanai data tattara waje ɗaya. Bakinta ɗauke da addu'ar samun nasarar amincewar Ummu abisa ƙaryar data shirya akan fitar ta fito. Daga inda Ummu take tako zubomata ido na alamar tuhuma. Gareta ta ƙarasa cikin danne komai da karsashin data aro. “Ummu kiran gaggawa na samu daga Ikram. Inaga dai abinda muka jima muna jirane ya fito”. “Amma Iffah....” “Ummu dan ALLAH kar kice a'a”. Iffah tai saurin tarar numfashinta cike da marairaicewa. “Ni ba hanaki zanyiba, sai dai wannan yawan fitar taki a kwanakin nan bana zuwa makaranta ba ya fara damuna Iffah. Shin kin manta halin da muka shiga da wanda zamu iya shiga a yanzu? Ina jin tsoro wlhy, matuƙar tsoro a duk sanda kika fita koda makaranta ne”. Sosai tausayin Ummu ya sake mamaye zuciyar Iffah, ta haɗiye hawayen da suka taru mata a ido tana ƙaƙaro murmushi. “Insha ALLAHU Ummu babu abinda zai faru, wanda ya farun ma a baya bazamu taɓa mu yafe ba. Fita ta kuma ta daina baki tsoro, tunda kinga duk sanda zan fitan ina suturta dukkan jikina”. “Shike nan ALLAH ya tsareki, dan ALLAH kiyi maza ki dawo kafin Abbin ku ya dawo gidan nan ko ɗan uwanki”. “Insha ALLAHU Ummuna”. Iffah ta faɗa tana rungumeta. Shafa kanta Ummu tai tana murmushin ƙarfin hali itama, dan ba wani zuciyarta ta samu nutsuwa bane ita dai, ta bartane kawai saboda tace fitar ta shafi karatunta. Amma zata cigaba da rakata da addu'a harta dawo.........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +22 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_9_* ...........Kasancewar wajene daba kowa ke shiga ba anyhow yasa sai da Iffah tai kiran Sir Fawzan bayan saukarta a bakin gate. Umarnin bama security ɗin wajen wayar ya bata. Bayan yayi magana da security ɗin suka bata damar shigewa batare data san miya faɗa musu ba. Tafiya take a nutse tana ɗan kallon wajen da tsarinsa. Dan babban garden ne mai cike da ababen kallo da ni'imtattun korayen ciyayi da ƙawatatun filawoyi. Ta taɓa shiga sau biyu a dalilin taron makarantarsu ta Islamiyya da aka gudanar a wajen. Ya riga ya faɗa mata inda zata samesa, dan haka kanta tsaye take nufar wajen ranta fes da nishaɗi tamkar ance mata ga wuƙa ga maƙoshin Tajwar Eshaan ta yanka. Sai da taje kusan ƙarshen garden ɗin ta tsaya, sai kuma ta shiga canki in canka na number wajen daya bata kasancewar akwai rukuni-rukuni na ɓoyayyun wajen hutawa da manyan mutane sukafi tu'ammali da su idan basa buƙatar wata hayaniya. Cikin ɗan ɗage kafaɗa ta nufi na farkon da zuciyarta tafi karkata. Ƙawatuwar wajen takai mai kallo shagala harya iya manta abinda ya kawoshi, kamshin firanni da wani iska mai busawa a hankali kaɗai na dabanne. Jitai kamar da shakku na shigowarta wajen, amma sai ta dannesa a ƙasan zuciya ta cigaba da takawa tamkar mai sanɗa tana leƙe-leƙe. Ta isa kusan tsakkiya zuciyarta ta shiga gargaɗinta ganin babu alamar akwai mutum mai numfashi a wajen, cak ta tsaya tare da ciro wayarta domin neman sir Fawzan. “Ya ALLAHU”. Ta faɗa jin ana sanar mata bata da kati kona sisi a wayar. Kamar zatai kuka ta sauketa daga kunenta tana ɗan ƙara danne-danne da cigaba da takawa a hankali batare data san mike a gabanta ba. Kaɗowar iska da sassanyan ƙamshin turare mai daɗin gaske ya sakata tsayawa cak ƙirjinta na harbawa da ƙarfi. Fararen idanunta ta janye daga kan wayar tare da ɗago kanta gaba ɗaya, a kan mutumin dake kishingiɗe bisa wani lallausan jan darduma daya haɗu da kalar korayen ciyayi ya bada ƙyaƙyƙyawan tsari ta sauke. Rabin jikinsa akan tum-tum yake. Kansa a risine yana kallon lap-top ƙirar kamfanin apple dake akan wani ƙaramin tum-tum ɗin itama. Gefensa kaɗan wani ƙyaƙyƙyawan bowl ne fari na tangaran, sai butar shayi kalar golden akan tray dake tabbatar da set ne dan harda ƙananun cups nashan shayi. Sanye yake da ƙananun kaya farare tas da suka fidda ainahin suffarsa ta masu ta'amalli da ƙarafuna, gashi sun sake fidda ainahin hasken fatarsa da sheƙinta irin na masu jin daɗi. Duk da tana a gab da shi aikinsa yake hankali kwance baiko nuna alamar yasan da zuwanta ba. “Mi kake buƙata?”. Sassaanyar muryarsa mai zurfi da kamewa ta daki kunenta da alamar akwai wanda yay tsammani ba ita ba. Ƙirjinta ne ya sake harbawa har tanaji kamar jininta daya tsinke na neman biyo hudojin gashin fatarta ya fito. Bata da niyyar cewa komai, gata tsaye tamkar an dasata ta gagara ɗaga ko ƙafa ɗaya tabar wajen duk da haka zuciyarta tafi buƙatar da tayi. Jin shiru ba'a amsa masa ba, ga tsaiwar mutum yanaji har yanzu a gabansa ya sashi ɗago lulu idanunsa masu haske da baiwar bakin ƙwayar tsakkiyarsu ya sauke a kanta. Komai tsayawa yay daga garesa, kamar yanda Iffah ma hatta kaɗawar iskar wajen ta tsaya mata cak... Fuskarsa dake a kame da kwarjini ya sake tsumewa yana sassauta girman idanunsa tamkar mai son lumshesu da gayya. A fisge, tamkar an jawo furucin daga bakin Iffah ta yamutsa fuskarta da ƙanƙance manyan fararen idanunta da tun a kallon farko ta kaudasu da ga kansa alamar kunya irin ta mace, “Idan ma kai aljanine wlhy nafi ƙarfinka. Wace irin jaraba ce duk inda nai saina ganka”. Ta ƙare maganar da hura bakinta. Kamar yanda bai motsa daga yanda yake ba haka bai ce mata komai ba, bai kuma janye idanunsa a kanta ba har yanzu. A zuciyar Iffah fa ta fara tsorata dajin tabbacin mutumin nan fa ƙila aljani ne. Amma sai taga idan ta nuna tsoronsa fa zai ma iya kasheta, saboda a yanzu haka ma ƙarfin hali take, tana matuƙar jin kaifi da tasirin idanunsa a dukkan ɓargon jikinta da jijiyoyi da gudanar jini. Amma sai ta dake a ƙasan ranta tana karanto addu'ar neman tsari da aljanu. Kusan tunani iri ɗaya ne a zukatansu. Dan shima dai zuciyarsa ta ƙara yarda wannan abar aljana ce kawai, yana ganin kuma ya kamata yasan miyasa take bibiyarsa ne?. Nisan data fara masa a idonsa ya fahimci tabar wajen, ilai kuwa can ya hangota tana tafiya cikin sassarfa ta nufi ƙofa. Cin karo data kusan yi da mutum ya sata ja gefe da sauri. Ɗaya daga cikin matasan datai masa gani biyu da su ne, cikin nuna alamar mamaki da tsuke fuska yake kallonta. Harara ta balla masa ta ƙyaɓe fuska da raɓashi ta wuce, danji take ƙafafunta tamkar ba'a kansu take takun ba..... “Fareedah!”. Da sauri ta juyo jin muryar Sir Fawzan daya sauke numfashi da dafe kansa na tabbacin ya jima yana nemanta. “Ina kika shigane wai? Tun ɗazun sai faman zagaye garden ɗin nan nake ni da securitys nemanki, ga wayarki ma taƙi shiga sam”. Maimakon ta bashi amsa sai ta zube a kujerar dake a kusa da ita ragwaf. A wahale tace “Sir ka bani ruwa nasha Please”. Sosai yanayinta ya sake neman firgitashi, amma fahimtar ruwan tafi buƙata ba tambaya ba ya sashi barin wajen da ɗan hanzari. Mintuna ƙalilan ya dawo da robar ruwa. Miƙa mata yay bayan ya ɓalle murfin. Tunda ta kafa kai bata koja numfashi ba sai da ta sha fin rabi, ta sauke robar tare da dafe goshinta tana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Lokaci ya bata sosai ta samu nutsuwa kafin ya kai zaune a kujerar dake facing ɗinta. “Fareedah miya faru wai? Ina kika shiga? Duk kin tadamin hankali saboda security sun tabbatar min kin shigo”. A hankali ta ɗago manyan idanunta da launin farinsu ya sirka ta zuba masa. Sai kuma ta janye da sauri tana girgiza kanta dan fuskar mutumin nan kawai ta gani a tare da shi saboda ta sakama ranta aljani ne. Idanunta rumtse tare da yakice tunanin ta sake buɗesu akansa. “Sir lokaci ya ƙure ina abokin naka?”. Ya fahimci bata son bashi amsa, sai kawai ya girgiza mata kai. “Rashin ganinki ya sakani a ruɗanin da har ya kira waya ban sani ba, sai daga baya na lura na kirashi shima kuma bai ɗaga ba”. “Ya ALLAH, shike nan itama wannan damar ta kufce min!”. “Bazamuce haka ba sai munji ta bakinsa, a yau ne dai kawai nake ganin bazai yuwu ba gaskiya, kodan ke a karan kanki ma. Kinga saura baifi mintuna arba'in ayi magrib ba. Kije gida, insha ALLAHU zanbi duk hanyar data dace domin ganin kin haɗu da shi”. Kallonsa take kamar zatai kuka. Sai dai saka zantukansa a ma'aunin hankali ya sata kasa cewa komai. “Kiyi haƙuri”. Ya faɗa cikin sake sanyaya murya yana mata wani lallausan kallo. Kauda nata idon tai daga kansa, taja iska ta fesar da jinjina masa kanta kawai. Dan ta tabbatar inhar tai magana kuka ne zai iya ƙwace mata ma..... *_MASARAUTA_* Gurfane take a gaban Uwa kamar yanda dokar take ga duk wanda ke binta. Duk da matsayinta da girmanta a cikin daular ruman a gaban uwa ita ba komai bace face mai neman biyan buƙata (Wa'iyazubillah). Kamar ko yaushe tsohuwar da suke kira uwa sanye take cikin jajayen kaya, sai dai saɓanin waccan ranar yau inuwarta kawai ake iya gani a jikin bangon ɗakin. Amma abin mamaki babu tsoro ko wata shakkar hakan a idanun hamshaƙiyar matar. Inuwar uwa ta kece da mumunar dariyarta mara daɗin saurare, kai kace za'a iya jinta a duk faɗin masarautar, sai dai abin mamaki iya ita ɗin kawai take jinta. Sai da tayi mai isarta kafin ta tsagaita tamkar ba'ita tayin ba. “Ta-ƙurya alƙawarina ya cika, zaku iya tunkarar kowa a yanzu da maganar auren Malik-alMuluk babu mai musa miki hatta Malikat da shi a karan kansa balle duk wani mai faɗa masa yaji. Sai dai akwai banbanci a wannan karon da baya. Hhhhhhhh!!”. “Umarninki shine abin jira Uwa mai share kukan mai kuka”. “Hhhhh Ta-ƙurya shiyyasa bana baƙin cikin taimakonki, zan kuma cigaba da taimakonki kiyita na sara keda duk mabiyanki. Ragamar kasancewar gida a hanun wasunki bashine zai sa su zama masu ƙarfin ikoba sama da naki. Ki shiga ki fita a haɗa gagarumin aure na bajinta tsakanin wannan yarinya da Malik-alMuluk. Hakan zaisa su shagaltu da tunanin komai ya canja musamman shafe watanni tara da Zawjata-almilki da suka rage suka kwashe gidan nan batare da ko ciwon kai ba. Ina son ki nuna bajinta irin wadda ko Malikat bazata yiba, Daular ruman zata cigaba da kasancewa a tafin hanunki a baɗini koda a zahiri kinada wanda suke nuna sunfi ƙarfinki. Ranar mako zata zama ranar sa'a Hhhhhhhh!!!”. Sautin dariyar ya cigaba da nesa da kunuwanta har inuwar uwa ta ɓace. Nannauyan numfashi ta sauke tare da murmushi mai nuna tsantsar farin ciki. Ta dubi ƙyaƙyƙyawan farin tafin hanunta da jini keta kaikawo tana sake maimaita kasantuwar daular ruman a tafin hanunta da uwa ta ambata mata. Tabbas ita ɗin mai sa'a ce, sa'ar da zata iya nunata a gaban duk wasu sa'ointa koma wanda suka ɗarata. Fatanta kawai ALLAH ya kaita ranar cikar burinta gaba ɗaya domin tabbatarma kowa dake cikin Ruman ma ba daular ruman kawai ba *Saka ƙwan kaza bashi ke nufin mallakar akurki ita ɗaya ba* sannan zuwan *mai guri bashi ke tabbatarda naɗewar mai tabarma ba*....... ★★_______★ Kwanaki biyu kenan Iffah bata sake neman sir Fawzan ɗinta ba, ta kuma kashe wayarta ta yanda shima koya nemeta bazai sametan ba. Ita tasan dalilin zaɓar yin hakan, duk da yanayinta ya nuna tana da damuwa dan babu walwala tattare da ita sam tun baro garden ɗin da tayi. Yau ma data kasance bazataje makaranta ba kamar yanda ta saba ta tashi taya Ummu aiki, sai dai yanda take komai kamar mara laka a jiki yasa Ummu nutsuwa a nazartar ta.. “Wai lafiyarki kuwa Iffah? Tun dawowar fitar da kikai shekaran jiya duk kin wani canja. Ko jikin naki ne?”. “A'a Ummu, kawai dai kaina na ɗan mun ciwo ne ƙasa-ƙasa. Amma na san barci ne da bai isheni ba”. “Barci kuma? To miya hanaki barcin?”. In'ina ta fara na rashin sanin abinda zata faɗa. Sai kuma tai ƙasa da kanta ganin yanda Ummu ta kafeta da idanu. Ummu mace ce mai yawan tsantseni wajen tarbiyyar ƴaƴanta. Komai tana binsa a sannu babu garaje ko gaggawar akan tafida yaranta tun kafin sukai haka, shiyyasa cikin sauki take iya sanin matsalolinsu da saurin fahimtar sabuwar hanya da suka ɗauka saɓanin wadda ta sansu da shi. Yanzu ma dai ɗauke kai tai ga Iffah ta cigaba da hidimar gabanta batare data sake magana ba. Daga baya ma saita ƙirƙiri jan Iffah da sabuwar hira da bata da alaƙa data farko. Tun Iffah na ɗararewa har ta saki jikinta... ★Washe gari ta ɗan danne kaso sittin cikin dari na damuwarta dan kar Ummu ta hanata zuwa makaranta. Sai dai koda taje makarantar ma dai zaune kawai ta kasance badan ta nutsu a fahimtar komai ba har aka tashi. Kanta tsaye ta fito domin samun abin hawa a bakin gate kamar sauran ɗalibai. Da ƙyar ta samu tare da wasu da suke kusan a anguwarsu, sai dai zasu rigata fara sauka... A hankali wata baƙar mota dake fake ɗan nesa da makarantar tasu ta fara bin bayan mai Mototaxi ɗin da sam shi hankalinsa baima kai ba. Haka suma su Iffah babu wanda ya kula da motar. Da mai motar ya fahimci zasu zargesa sai ya canja salon bin nasu. A haka har aka sauke abokan tafiyarta. Motar ta cigaba da binsu har titin anguwarsu, anan aka dakata har mai Mototaxi ɗin ya shiga ya kai Iffah ya juyo zai fita suka tsaidashi..........✍ _To ke kuma baƙar mota daga ina🙆🏻?._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_10_* ........Kamar wasa Iffah na shigowa gida ta zube kwance tana rawar sanyi, ga jikinta ya ɗauka matsanancin zafi. Ummu bata kawo komai a ranta ba game da ciwon Iffah sai tunanin ranar da ake ƙwallawa ce ta washeta. Da ƙyar ta tilastata tai wanka, taci abinci kaɗan ta ajiye. Maganin zazzaɓi Ummu ta bata tasha, daga haka ta koma ta kwanta ranar ko Islamiyya bataje ba. Da dare firgita data dingayi saboda munanan mafarkai ya sa kusan kowa bai rintsa ba a gidan sai gab da asuba. Da barci yaɗan figeta saita tashi a firgice har sai sun rufeta da addu'oi take samun nutsuwa ta sake komawa barci. Al'amarin ya tsayama kowa a rai, sai dai ganin ta tashi ragal da asuba tai salla sai sukaita mamaki. Dan bazaka taɓa tsammanin itace a daren jiya ba. Da safe koda tace zataje makaranta hanata Babiy yayi, acewarsa ma asibiti zasuje da Hanash. Kasancewar Iffah da rashin son asibiti sai ta turje akan itafa ta warke, dama jiyan rana ce (ta fake da abinda Ummu tace). Ganin harda ƴan kwallanta Babiy yace to inhar zazzaɓi ya sake dawowa a yinin yau dole suje asibitin nan. Da sauri tace ta yarda. Bayan wucewar Babiy tai ta ɗan ƙarfafa kanta harda taya Ummu aiki, duk da yanda takejin yanayinta babu daɗi haka tai ƙudirin shirin Islamiyya idan lokaci yayi, tana ɗaki kwance bayan idar da sallar azhar sai ga kiran malaminta Fawzan, wayar kawai ta tsurama ido tamkar bazata ɗauka ba harta katse, wani kiran ya sake shigowa shima harya katse bata ɗaga ba. Duk da zumuɗin son ganin kiran nashi da take ciki a kusan kwanaki uku sai taji hanunta ya mata nauyin ɗagawa a yanzu daya kira... Shigowar saƙo ya katse mata tunani, ta kai hannu kan wayar ta ɗauka kamar mai tsoro... _“Fareedah ga dama ta biyu ta sake samuwa, Idan kinga saƙona kiyi ƙoƙarin fitowa kafin Four”._ A zabure ta miƙe jikinta na tsuma ta hau shirin Islamiyya, tare da tattare dukkan takardun bayanan da take ta faman adanawa harma da waɗanda ta ƙara haɗawa a kwanaki ukun nan. “Ummu zan wuce Islamiyya”. Ta faɗa lokacin da take ƙoƙarin saka takalmi a ƙafarta Ummu na tsakar gida tana alwalar sallar la'asar. “Ke da baki da lafiya auta”. “Ummu naji sauƙi wlhy, kinga saukarmu ya kusa babu buƙatar na fara wasa ai. Malam nata mana gargaɗin hak......” Sauran maganar ya maƙale a harshenta sakamakon tashin sautin busa mai nuni da isowar jama'ar masarautar Daular Ruman. Tamkar an daki kan Iffah da guduma haka taji wani dummm! A cikin kunnenta har suka ƙarasa shigowa cikin gidansu jinta bai dawo ba. (Shin tsoro ne? Ko firgici?) bata san wanene ya risketa ba...... Taɓata da Ummu tayine ya sata jan kakkauran numfashi tare da kallonta. Jikin Ummu ne ke rawa, idanunta kam tuni sun tara ƙwalla. Iffah ta shiga girgiza mata kai alamar kar tai kuka, ta sake damƙe hanunta cikin nata tare da maida kallonta garesu rai ɓace, dan ta ɗauka alwashin a wannan karon komi sukazo da shi sun tara sun samu, sai dai a kasheta... “Mi kukazo yimana a gida kuma? Ko kun dawo muma ku idasa kashemu tamkar yanda kuka halaka min ƴan uwana da tsafink......” Da sauri Ummu ta danne mata baki da tafin hannunta tun kan ta ƙarasa faɗa. Kai take girgizamata cikin rawar jiki. Da ace ba Ummu bace babu abinda zai hanata ta ture hanunta ta ƙarasa abinda ta fara faɗa ko zata samu salama a ranta. Sai dai kuma bazata iya ba, dan haka ta shiga yima Ummu alamar roƙo da magiyar ta barta amma taƙi yin hakan... Basamuden nan ne na kullum mai riƙe da bulala ya daka mata tsawa. Da sauri Ummu ta sakemata baki, sai dai ta jawota jikinta ta ƙanƙame. Iffah jitai zuciyata ta ƙara hautsunowa, a matuƙar zabure ta sake buɗe baki zatayi magana ya dakatar da ita... “Ke ƴar talakawa lura da inda kike. Bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane. Idan taƙamarki tsageranci tamkar ƙiftawar ido za'a sauke miki shi, a kuma shafe babinku daga ke har iyayen naki a doron ƙasa”. Hasala iya hasala Iffah tayi, Kukan da Ummu ta fashe da shi ya hanata cewa komai ta juya gareta jikinta na rawar shiga tsananin ɓacin rai, kanta take juyamata alamar karntace komai..... “Umm....” “A'a Iffah! Ina umartarki karki ce komai”. “Kibarta tace ɗinma yanzu harshenta ya zama datsatstse a gabanki.” Kafin Ummu dake girgiza kai tace komai Babiy ya shigo tamkar an jehoshi, da alama dai wanine ya sanar masa da zuwan jama'ar masarauta gidan nasa. Ko sau ɗaya basu bashi damar cewa komaiba suka isar masa da saƙon kira daga daular ruman. “Innalillahi.....” Iffah ta shiga ambata ita da Ummu, dan sunaji a ransu tarihine dai yake ƙoƙarin maimaita kansa, hawaye masu tsananin ƙuna da ɗaci na gangarowa bisa ƙyaƙyƙyawar fuskata Babiy da shima dai yasan labarin gizo bazai wuce ƙoƙi ba. A gaban idonsu aka wuce da Babiy Daular Ruman a karo na uku, tare da barin wasu dakaru a ƙofar gida ta hanyar hana duk wani mai yunƙurin fita daga gidan. Haɗe kai kawai Iffah da Ummu sukai suna kuka, dan shi kaɗai suke da damar yi ɗin.. ★Bayan cikar awanni biyu da tafiyar Babiy sai gashi ya dawo, dawowa irin wadda ya saba a duk lokacin da makamancin kira irin wannan ya samesa daga daular Ruman. Yanda ya kafe Iffah da idanunsa dake zubda hawaye ya saka Ummu zubewa ƙasa cikin kuka. “Abu Hanash itama zamu rasata ko? Itama ka ɗaura mata aure da Tajwar.....?” Hawayene masu ɗumi da ƙuna suka ziraro a idanun Babiy, ya girgizama Ummu kansa a hankali alamar a'a, tare da girgiza kan nasa kuma alamar tayi shiru. Hawayen nata ta share kamar yanda ya buƙata, sai dai jikinta bai bar tsuma ba. Kamar yanda Iffah data kafesa da idanu bata iya ko ƙyaftawa ba. Ummu ta sake gyara zamanta da fuskantar Babiy da ƙyau.... “Idan ba abinda muke tunani bane to minene ya faru?”. “Ki kwantar da hankalinki babu komai f.....” “Bazan taɓa yarda babu komai ba. Sai dai idan kana so ka rufeni ne. Hakan kuma shine mafi ƙololuwar kuskuren da banajin zan iya yin afuwa gareka a kanshi. Dan inaji a jikina zuwanka masarauta nada nasaba da rayuwar yarinyata data rage min, idan har zuciyarka ta iya ɓoyewa ƙwayoyin idanunka basu lulluɓe komai ba, garama ka sanar min”. Babiy ya fahimci idon Ummu ya rufe ta manta Iffah na wajen, dan haka ya cigaba da ƙoƙarin ganin ya kufcema faɗar abinda yazo da shi har sai sun keɓe amma ta dage akan itafa ya faɗa mata a yanzu. So yake ya buɗe ido amma bashi da sauran ƙarfin zuciya a yanzu, dan haka a sanyaye ya rumtse idanunsa da launinsu yay matuƙar komawa ja. “Ba'a ɗaura mata aure da shi ba. Sai dai....” ya kasa ƙarasawa. “......Sai dai me? Dan ALLAH ka faɗa min”. Ummu ta faɗa tana mai sake fashe masa da kuka mai matuƙar sake ɗaga masa hankali. Miƙewa yay yunƙurin yi tai saurin riƙe masa ƙafa. Babiy ji yake shima kamar ya fashe da kuka ya huta kawai. Ya dawo ya durƙusa gaban Ummu tare da riƙo mata hannu, “Akan abinda suka faɗa munada mafita tunda yasha ban-ban dana baya Jumaima. Dan haka na gama yanke shawarar zamu bar garin nan dama ƙasar gaba ɗaya a daren yau insha ALLAH. Dan sun buƙaci izinin neman auren Iffah ne a gareni, sun kuma bani damar zuwa nai shawara daga nan har zuwa ƙarshen makon nan”. Kafin Ummu ta samu damar cewa wani abu sulalewa da faɗuwar Iffah a lokaci guda ta riski kunnuwansu. A tare suka zabura kanta jikunansu na matuƙar rawa da tsuma. Ummu ta fashe da kuka dai-dai tana ɗago Iffah dake wanwar a ƙasa taga ta koma yaraf alamar babu rai a tare da ita..... .....Sosai kukan Iffah ya sake ɗaga hankalin Babiy. Dan tunda aka zuba mata ruwa ta farfaɗo ta haɗe kai da gwiwa. Suma idanu kawai suka zuba mata suna hawayen zuci, rikicin yana a kantane kawai, amma sune suka fita jin raɗaɗin a zuciya saboda ita akwai ƙuruciya tare da ita. A ganinsu bai zama lallai ma tana hange irin wanda su suke matane ba. Kusan mintuna talatin suna a haka, kafin Babiy yay ƙarfin halin miƙewa suma yay musu umarnin su tashi su koma ciki. Sai da taimakon Ummu Iffah ta iya miƙewa, har sun kusa shiga ɗakin ta tsaya, ɗagowa tai ta dubi Ummu ta juya ta dubi Baby hawaye na sauka da gudu bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarta. “Bazamu gudu ba Babiy, zan aure shi....” Kaɗan ya rage Babiy yaci uban tuntuɓe saboda firgitaccen furicin Iffah mai kamanceceniya da gawurtaciyar sautin saukar aradu cikin tsakkiyar duhuwar dare. Ummu ma dai da taima Iffah sakin bazata ƙirji ta dafe dukanin idanunta na firfitowa..... Iffah ta share hawayenta da sakin murmushi a karo na farko. “Ummu! Babiy! ku kwantar da hankalinku, kar kuma ku ɗauka ba'a cikin hayyacina nake ba. Nasan burinku shine ku kuɓutar dani daga mutuwa, sai dai kuma a duk inda zanje ku sani tana tare da nine. Wannan azzalumin ba guje masa ya kamata ayi ba, tunkararsa ya kamata ayi. Kamar yanda kaka ya faɗa, a wasu lokutan gujema ƙaddara ba mafita bace sake kirawowa kai halaka ne. Amma tunkararta gaba da gaba ƙarfafa imani ne sannan jarumtace. Shin idan mun gudu kunada tabbacin zamu iya tsere musu bayan ƙasar a hanunsu take? Sannan idan mun tafi ina zamuje bayan babu inda muka sani sama da ƙasar Ruman. Fir'auna ma da yay nasa zamanin mulkin da ko kama kafarsa wannan shaiɗanin baiyiba UBANGIJI maida ANNABI MUSA (A.S) yay cikin gidansa ya rayu bisa ƙudirarsa da tabbatar masa shine mai iko akan kowa da komai. Azzalumin nan ba gudun masa ya kamata ayi ba, daƙilesa ya kamata ayi, domin idan ni kun kuɓutar dani, su sauran iyayen da zasu iya fuskantar makamancin halin da kuke ciki fa bayanku?. Babiy zanyi biyayya kamar yanda ƴan uwana sukayi, kuma ku sani da iznin ALLAH nice zan kashes........” Cikin rawar jiki Ummu ta zaburo tare da toshe bakin Iffah. Sai faman waigen bayansu take domin sanin dakarun Daular Ruman na ƙofa gidan har su biyar. Babiy ma gaba ɗaya kalaman Iffah sun sake rikitashi. Sai dai kafin wani cikinsu ya samu damar cewa wani abu ta shige cikin ɗakin. Idanu suka tsirama juna shi da Ummu harna tsahon mintina biyu, kafin Babiy yay ƙarfin halin janyewa yana mai jan nannauyan numfashi da barin wajen ya shige ɗakinsa. Da ƙyar itama Ummu ta sauke numfashin, har zatabi bayan Iffah sai kuma ta fasa ta nufi ɗakin Babiy ɗin itama. Shigowarta dai-dai dayin sallamarsa waya manne a kunensa. Zaune takai a bakin gadon dake ɗakin dan inba haka ba zata iya zubewa ƙasa saboda yamutsawa da jininta ke mata. Jin sunan Baba da Babiy ya ambatane ya sata maida hankali garesa itama. Komai sai da Babiy ya zayyanema Kaka kafin yay shiru alanar saurarensa. Daga can Baba yaja nannauyan numfashi bayan gama sauraren surukin nasa mijin ƴarsa tilo data rage masa a raye. Sai kuma yay murmushin ƙarfin hali mai sautin daya isa har cikin kunnen Babiy. “Ni ma ina goyon bayan maganar Fareedatu. Da ace wani rai nada ikon hana tabbatuwar wasu daƙiƙu na gaban rayuwarsa masu tafe da ƙaddara da mutane da yawa sunyi rigakafi kafin cikar adadin waɗan nan daƙiƙu Muhammadu Zayyanu. Amma inaso ku tuna muɗin talakawansu ne, masu rayuwa a ƙarƙashin mulkinsu, bamu da wani ƙarfin iko akan hukuncinsu garemu ko kan ƴaƴanmu. Dan haka ku bita da addu'a kawai itama.” Tamkar yana gabansa ya jinjina masa kansa, tare da ƙoƙarin danne hawayen da yake na zuciya da ƙunarsu gara ace a zahiri suke zuba bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarsa. “Shikenan Baba, amma furucin Iffah ya girgizani, ina tsoron kar zuciya ta ingizata tai yunƙurin aikatawa. Kisa fa! Koda bata aikata ba fitar wannan furucin zuwa kunen wani bayan mu ba ƙaramar magana bace” “Kar komai ya dameka Muhammad Zayyan. Ta faɗane kawai saboda raɗaɗi da takeji da kuma ƙuruciya, kai dai ka sanar dasu ka amsa daga nan zuwa kwanaki uku. Zan zo a amsa kuɗin auren da ni dama wasu a cikin zuri'an ka insha ALLAHU.........✍ ALLAH sarki Iffah kin bani tausayi🥲 *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_11_* ..........Iffah taci kuka matuƙa da ko maƙiyinta ya dubeta sai ya tausaya mata. Sai dai kuma iya juyawa su Babiy sun mata akan su gudu ta kafe akan itafa ta yarda zata aura *_Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-Majeed_*. Sosai hankalinsu yake ƙara tashi da tirjewarta. Gashi gaba ɗaya ta bikice musu ko isashen lafiya babu a tare da ita. A cikin wannan halin Babiy ya sake samun saƙon kira daga masarauta. Yana shirin tafiya sai ga Kaka. Duk sunyi matuƙar mamakin zuwan nasa, dan abune mai wahalar gaske a garesa zuwa inba da wani dalili ba. Sun tarbesa kamar yanda suka saba matsayinsa na uba. Bayan gama gaisawa ya kai dubansa ga Iffah dake kwance cikin bargo duk ta rame ta sake komawa fayau da ita, dama tun rasa ƴan uwanta ɗan jikinta ya zube, dan sam ba siririya bace. Iffah nada jiki murjajje daba za'ace mata siririya ba kuma babu mai sakata a sahun masu ƙiba. Duk da shekarunta har yanzu sunada ƙaranci ALLAH ya bata jiki na manyan mata da'a yanzu komanta yake ciff dai-dai da halittarta. Kaka ya ɗauke idanunsa a hankali tare da maidasu ga Babiy. “Muhammadu Zayyanu ka sakama ranka nutsuwa ka cire batun barin gidan dan bashine mafita ba. Hasalima tun randa ka amsa kiran masarauta wannan gidan zagaye yake da dakarun daular ruman harta inda baka zata ba. Ko'a tunaninka zasu tunkareka da wannan maganar su baka damar kanka sannan su koma gefe da tunanin kai bazakayi wani yunƙuri ba”. Daga Babiy har Ummu da Hanash kallon tsoro da mamaki sukema Kaka. Ya ɗan jinjina kansa alamar tabbatarwa. “Karku damu da yanda akai nasan wannan, kai dai kawai kaje ga kiran da sukai maka. Karka kuma nuna wani ja'inja kace ka amince musu suzo neman auren”. Kuka Ummu ta fashe da shi tana kallon mahaifin nata. Yay ɗan murmushi da ɗauke kansa tamkar bai fahimci mitake nufi ba. Ganin haka Hanash da idanunsa sukai jajur cikin cinkushewar harshe yace, “Amma kaka miyasa ka zaɓa itama mu sake rasata? Wlhy nayi alƙawarin in har itama ta salwanta sai na salwantar da ran Shahan-shan da wannan hanun nawa wajen ɗaukar fansa koda nima za ai gunduwa gunduwa da naman jikina!!”. “Ba kai ne zaka salwantar da ruhinsa ba, ni nan Fareedah bint Zayyan nice zan karya ƙarfin ikon azzalumi da hannuna, zan masa shaƙa irin wadda har sai ya mutu yana mai kallon tsakkiyar cikin ƙwayar idanuna Hanash Akhi”. Su duka zuba mata idanu sukayi, dan a yanda take maganar babu alamar tana a cikin hayyacinta. Babiy zaiyi magana Kaka ya girgiza masa kai alamar kar yace komai yaje kawai.... ★Kamar yanda Kaka ya umarci Babiy ya amsa kiran masarauta kasancewar a wannan karon an bashi damar zuwa ne shi kaɗai batare da dakaru sun taho da shi ba. A yanda ya samu tarba zai tabbatar maka dama a jirace ake da zuwansa. Kamar ko yaushe a wannan karon ma baiga Tajwar ba, amma dai a karon farko na tarihin rayuwarsa an kaisa har cikin fadar Shahan-shan. Inda yaga tsantsar dukiya da ainahin karagar mulki ta Shahan-shan da akayita da zallar zinare. Hakan ba'abin mamaki bane ba, saboda girman Shahan-shan koda da diamonds akai kujerar mulkinsa bazai zama wani babban al'amari ba, sannan zinare arziƙin ƙasar su ta ruman ne da bare ma kanzo ya ci balle su ƴan ƙasa musamman Shahan-shan. Karo na farko da Babiy yaga karramawa daga dattijan daular ƙasar ruman. Waɗan da ko'a mafarki bai taɓa tunanin gani ba dan su ɗin ma ba'abune mai sauƙi ga duk wani talaka ganinsu ba kai tsaye haka. Duk da a birkicen da yake ALLAH sai ya saka masa nutsuwar yi musu bayani babu ko rawar harshe a tare da shi. Sun masa godiya da tabbacin a gobe idan ALLAH ya kaimu masu neman aure zasu zo. Karramawar da sukai masa ta matuƙar basa mamaki da tsayawa a ransa, sai dai ta wani gefe na zuciya ya tabbatar da sabuwar hanyar yaudarace kawai. Cikin danƙareriyar mota aka maidasa har gida badan yaso haka ba, yayi shiru ne kawai domin bin unarnin mahaifin matarsa, dan duk da bai taɓa ambatawa ba ga kowa ya jima da tsanar duk wani abu daya shafi masarautar daular ruman.. ★A wannan dare Babiy yayi zaman kuka irin wanda ake kira kuka a zahiri da baɗinin rayuwa. Har yanaji bazai iya cigaba da yima kaka biyayya ba shikam, zai ɗauke Iffah su gudu daga ruman koda daga shi sai ita ne. Sai dai wani ɓangare na zuciyarsa na tunatar da shi maganar Kaka, yasan gaskiya ya faɗa, dan daular ruman bazata zuba ido na barinsa sakakai ba. Ajiyayyun dakarun dake a ƙofar gidansa ma kawai tabbaci ne.... A ɓangaren Ummu ma bata runtsa ba, sai dai saɓanin Babiy ita kwana tai tsaye tana gayama UBANGIJI damuwarsu da roƙonsa kariya da kuɓuta ga yarinyarta. Shi kuwa Hanash kwana yay ƙulla ta yanda zai halaka Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed da kansa. Hakama Iffah nata shirin nada alaƙa dana Hanash. Ta gama yankema kanta koda zata mutu itama sai dai su mutu tare da Tajwar Eshaan. In yaso a binne gawarta a tsakiyyar ruman matsayin tarihin da za'a dinga tunawa....... *_WASHE GARI_* Washe gari data kasance safiyar laraba da misalin ƙarfe biyar na yamma sai ga manyan baƙi daga masarauta ruman. Baƙi masu ban mamaki, dan kuwa wasu manya ne a cikin dattijai masu faɗa aji a daular ruman. Sannan iyaye ga Shahan-shan ta ɓangaren jini makusanta sosai ga mahaifinsa. Tamburan masarauta da ɗunbin tawagar hadimai da jibga-jibgan motoci da suka ƙoshi ne suka tabbatarma da jama'ar anguwa dama maƙwaftan anguwar wace tawagace. Tuni mutane suka fara ƴar rige-rigen fitowa daga gidajensu bama idanunsu abinci. Sun tarbesu bisa jagoranci Kaka daya tsara komai tare da shimfiɗa kakkauran gargaɗi ga su Babiy. Bayan an musu masauki a cikin lambun Babiy ta ɓangaren garden ɗin da yayi domin farin ciki ga iyalansa aka cika musu gabansu da ƴaƴan itatuwa duk da babu tunanin ko zasu ci. Babiy, Kaka, da wasu dattijai biyu, ɗaya ta ɓangaren Babiy, ɗaya ta ɓangaren Ummu ɗan uwa ga kaka kenan suka zauna da su. Sun miƙa gaisuwa a garesu cikin mutuntawa da nuna tabbacin su ɗin masu ƙarfin iko ne a garesu talakawan ƙasan ruman. Hakan yayima dattijan matuƙar daɗi da yabama su Kaka. Dan haka suma suka nuna mutuntawa a garesu da basu ƙarfi matsayin waɗanda sukazo neman iri wajensu. Hakan ya ɗan bama su kaka mamaki amma sai babu wanda ya nuna. Sun gabatar da buƙatarsu, tare da bada duk wani abu na al'adar aure da ƙasar ruman ta tanada ninki wanda akanyi sau goma. Hakan sai ya ƙara firgita Babiy da bashi tabbacin yanda za'a salwantar da rayuwar ƴarsa ɗaya tilo data rage masa zai zama ƙololuwar girma fiye da ƴan uwanta kenan. To inbaice hakaba mizaice, dan dukiyar da suka kawo kawai tamafi ƙarfin ma sayen Iffah idan sayarwar zaiyi. Bai samu damar cewa wani abu ba, yadai cigaba da kukan zucinsa yabar su Kaka dayin abinda ya dace. A wannan zama aka ƙarƙare komai har ranar ɗaurin aure dama inda za'a ɗaura auren. Daga haka sukai addu'a suka tafi bayan an shigo da tarin kayayyakin da sukazo da shi. Daga Babiy har Ummu tagumi kawai sukai suna kallon kayan da aka baza a tsakar gida. Hakama Hanash da dattijan nan guda biyu da sai gobe zasu koma tare da kaka. Kaka kuwa na gefe zaune abinsa tamkar baima san mike faruwa ba a gidan. Yayinda Iffah ke can ƙuryar ɗakin Ummu kwance cikin zazzaɓi data yini da shi..... Washe gari su kaka suka wuce batare daya sake cewa uffan ga su Babiy ba akan komai. Yadai gargaɗi Babiy akan karya kuskura yace zai yi wani yunƙuri. Ya kuma sakasu killace dukkan kayan da aka kawo daga masarauta..... ★★★_______★ Tamkar da gayya cikin kanƙanin lokaci gari ya ɗauka Shahan-shan zai yi aure, alamu kuma sun nuna ana shiryama auren da shiri na musamman duk da amaryar bata kasance ƴar kowa ba. Hasalima ahalinta nada tabon Shahan-shan a dalilin salwantar ƴaƴansu biyu kafin ita. Dukkanin waɗan nan ƙananun magana na faruwane a bakunan mutane da ƙaramar murya, yayinda a kafafen ƴaɗa labarai da fejikan yaɗa zumunta babu mai iya ɗaga murya yayin faɗa sai fatan alkairi kawai. Mutane sun sake samun tabbacin wannan aure na musammne daya sha banban dana baya sakamakon fara shelarsa a kafafen yaɗa labarai domin gayyatar manya-manyan ƙasar kamar kowane Tajwar da jama'ar majalissarsa da talakawan garinsa. Da yanda ake wasu ƴan gyare-gyare a daular ruman wai duk na tarbar zuwan ranar ɗaurin aure ne. Humm abin faɗa taf bakunan mutane sai dai babu damar faɗar. Idan kuma suke ganin zasu sami wani ƙarin bayani an toshesa dan babu mai ikon shiga gidan Babiy a halin yanzu kasancewar zagaye yake da dakaru tako ina, acewarsu suna bama *_Zawjata-almilki_* tsaro ne. A cikin gidan kuma babu mai fita hatta da Hanash dake zuwa babbar makaranta... A haka kwanakin biki da suka rage suka cigaba da shurawa batare da wadda ake iƙirarin zama amaryar ta sake tada kai ta dubi wani abu daya shafi auren nata ba koda da kallo. Ta dake matuƙa tamkar ba itaba, hatta da ciwon dake cinta a tsaitsaye taki bada damar da su Ummu zasu fahimta. Ta ƙeƙashe idanunta ƙam ta hana hawaye zuba daga cikinsu. Ta tattare gaba ɗaya hankalinta ta maida ga rubuce-rubuce da babu wanda ya fahimci na minene a gidan, dan bata bari kowa ya duba mata shi. Sai dai ga duk mai hankali a duba ɗaya da zai mata zai fahimci tana cikin matsananciyar damuwa, mai busar da zuciyar mai ita da zai iya aikata komai da zai iya zama komai akan komai.. Kamar ko yaushe yau ma bayan ta kammala ayyukan gidan da take taimakawa Ummu da su ɗaki ta koma tana kukan zuci daya zame mata abokin rayuwa. A idaniyarta kam babu alamar ɗigon hawaye, sai dai raɗaɗin wanda ke kwaranya a zuciya ya maida launin idanunta sirkin ja har kana iya ganin jijiyoyi a cikinsa. Duƙufe take akan littafinta tanata rubutu da sakin ajiyar zuciya akai-akai. Ummu data shigo ɗakin takai zaune a kusa da ita tana mai tsurawa rubutun idanu na wasu sakanni. “Ibnati!”. Karan farko Iffah ta ɗago ta kalla Ummu duk da tun shigowarta ta jita sarai. Wani irin miskilin murmushi ta saki tare da maida kanta a hankali ta duƙar.. “Kina ganin laifinmu ko?”. Cak ta tsaya da rubutun data cigaba, sai kuma ta saki murmushi. Tsahon sakkani uku kafin ta ɗago ta dubi Ummu. Ta ɗan girgiza kanta da ajiye biron hanunta. “Ummuna idan har zanyi zargin wani akan wannan al'amarin to kaina ya dace na zarga. Ku ɗin nagartattun iyayene abin alfaharin kowane irin ɗa. Ni ya dace nazo muku da wannan maganar, domin nice na saka zukatanku a damuwa da ɗunbin fargaba. Na tabbata a kowane sakan, a kowane minti, a kowane awa, a kowane kwana na waɗan nan kwanakin kunayinsa ne cike da fargabar shuɗewarsu da gabatowar su. Kuyi haƙuri ku ƙara haƙuri ku gafarceni. Koda baku faɗamin ba, baku faɗama duniya ba nasan irin raɗaɗin da kukeji a zukatanku domin nima makamancinsa nakeji. Sai dai ina muku albishir Ummuna, koda zakuyi kuka a wannan gaɓar bazakuyi irin na baya ba. Na muku alƙawarin kukan ku zai kasance tare da dariyarkune a lokaci guda. Dan ruhina sai ya amso muku diyyar su Nina Arfa kafin yabar gangar jikina. A duk randa saƙon mutuwata zai riskeku insha ALLAHU zai riskekune tare da na mutuwar azzalumai. Dan haka ina roƙonku kar kuyi baƙin ciki a wannan karon, zaku sadaukar da ruhin da zaije muku yaƙin neman ƴancin kai ne ku da al'ummar ƙasar ruman.....” Kai Ummu ta shiga jujjuyawa hawaye na kwaranya a idanunta, “Ibnat...” “Na roƙeki kar kice komai Ummuna, albarkarki itace mafi ƙololuwar buƙata ga ruhin daya daɗe da zama cikin tahin gawa. Ƙaddarata rubutacciya ce tun daga alƙalamin da idan yay rubutu babu wani duster dake iya gogesa”...........✍ ALLAH sarki Iffah, ALLAH ya baki damar yaƙi irin wanda ya dace da fatanki na alkairi🙏🏻😭 *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_12_* .........Kalaman Iffah sun zama mafi ƙololuwar zama famin gyambo a zukatan Ummu da Babiy harma da Hanash. Sun zanu da zanen da zuciya ta killace koda tunasu zai zama mai raɗaɗi a cikinta. Sun karɓa domin karɓar ta zama tilas a garesu saboda rashin murya da ƙarfin iko da suka rasa a hannayensu. Sun cigaba da kuka saboda kukan shine kawai mafita a garesu. A haka kwanaki suka cigaba da tafiya da raunin zukatansu har zuwan ranar juma'ar da masu ƙarfin iko suka tsaida matsayin ranar ɗaurin auren ƴarsu. Bayyana ko misalta kasancewar wannan dare da wayewarsa ma ɓata lokacine game da halin da ahalin malam Zayyan suka tsinci kawunansu. Babu wani alamomin biki daga ɓangarensu sai ma zaman makoki. Dan bayan Iyyani da Kaka da wasu dattijai da basu gaza biyar ba a cikin zuri'arsu babu wanda ya halacci wannan makahon aure hatta da maƙwaftansu. Bisa tilastawar Kaka Babiy da Hanash sukai shirin halartar massallaci yin sallar juma'a da riskar abinda zuciyoyi ke tsananin ƙuna a kansa. Sun tafi sun bar Ummu da Iyyani da tazo itama a yanayi mai ban tausayi. Amarya Iffah kam idanunta ma babu wanda ya gani a wannan safiya abinci ma Iyyani ta bita da shi har ɗaki.... *_TAFARU TA ƘARE_* Bayan gushewar wasu awanni, masu tafiya da ƙarfin bugun zuciya busa irin ta sarakai da tashin tambura ya karaɗe cikin birnin Daular Ruman dake cike da manyan baƙi tako ina. Dan kuwa sarakuna goma cif na ƙasar Ruman duk sun halarta duk da suma akwai raɗaɗin rasa ƴaƴayensu a zukatansu har yanzu. Koda yake wasu a ciki sun bada ne da kwaɗayi na burin zamowar ƴaƴan nasu zama matan Shahanshan, suna ganin hakan wani ɗaukaka ce a garesu da samun wasu damammaki...... Iffah dake kwance a ɗaki zuciyarta a bushe, idanunta dake zubda hawaye a ɗazun a soye ta jiyo bayanin ɗaura aurenta da Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-Majieed daga bakin su Kaka. Wani irin dimmm taji a cikin kunnuwanta tamkar ɗaukewar wutar lantarki daga tashar gidan redio, ta koma ita ba wadda ta suma ba, ba kuma wadda ke a raye ba tsabar tsintar kai a wani hali. Ta jima a haka kafin ta dawo hankalinta kwakwalwata ta fara tantance abinda taji ɗin. Kenan abinda ya faru da yan uwanta a wasu watanni da suka shuɗe itama shine ya faru da ita yau? Itama zata mutu mutuwar rashin gata da ƴanci a hanun azzalumin mai mulkin Ruman da jama'ar cikinta. Daga yau za'a koma ƙirga mintuna da daƙiƙun mutuwarta da suka rage mata, daga yau tayi bankwana da Ummu, da Babiy, da Hanash Akhi da su Kaka. Anya kuwa zata iya? Anya kuwa sadaukarwar nan ta dace da rubutattun burukanta? Anya kuwa zata iya jurewa? Kai ina bazai yuwu ba. (Mizai hanasa yuwuwa? Bayan zakije inda ko kuwwa kikai babu maijin muryarki?) wata zuciya acan gefe ta ayyana mata. A karo na farko hawaye masu zafi da raɗaɗi suka silalo bisa kumatunta da gudu. “Dole ma na jure, jurewa irin wadda a duk faɗin duniya labarina zai karaɗesa a lokacin dana hukunta Tajwar Eshaan ibn Haysam ibn Abdul-majeed”. Ta faɗa cike da ƙwarin gwiwa na tabbatar da burin mai ɗaukar fansa. Batare data goge hawayen dake cigaba da rige-rigen zubo mata ba ta sauka a gadon tana tangaɗin jiri. Wayar data maida ta ajiye da ƙudirin ta daina amfani da ita ta lalubo, haɗata tai ta kunna, sai dai tai ɗan jimm namai nazari kafin ta fara rubuta saƙo. Minti biyu bayan turawa kira ya shigo. Numfashi ta fesar, sai kuma ta saki murmushin takaici jin abinda aka faɗa daga can. “Sir bamu da lokacin tattauna wannan a yanzu”. “Na sani Fareedah, sai dai inajin matuƙar tsoro, tsoro irin wanda ko'a ido aka kalla an san tsoro ne. Nasan na rasaki na har abada a yanzu”. Murmushin takaici ya suɓuce ma fuskarta, sai dai ta hana hawayen da suka ciko mata ido zubowa. “Wannan shine tsoron dana gudar maka fuskanta tun farko dama duk jama'ar Ruman. Amma bazan gajiya ba, plan A dama yaƙin sunƙuru ne, plan B mafi haɗari amma da yaƙinin nasara”. “Ta yaya Fareedah? Kin san kuwa waye Shahanshan? Kin san minene girman ikonsa?.....” “Na sani mana tunda nima a ƙasar aka haifeni. Sannan na zama cikin ahalin da sukafi ɗanɗana ɗacin girman ikon nasa da zalunci. Karka damu da haɗari sir, taimako ɗaya zakamun a wannan plan ɗin wanda babu wani abu da zai shafeka da iznin ALLAH”. “Amma Fareed....” “Please sir”. Kakkauran numfashi yaja ya fesar cike da ƙarfin halin son danne rauninsa a gareta. “Okay ina jinki”. “Ka bani number abokinka”. “Fareedah mi kuma ya rage?”. “Abubuwa masu yawa da amfani, hasalima yanzu ne za'a fara wasan na gaskiya”. “Karki taurin kai”. “Na jima da zama mai busashiyar zuciya”. “Ki fahimceni”. “Ko kaina ma bana iya fahimta sir”. “Bana son na rasaki Fareedah”. “Iyayena sun jima da haƙurin rasa ni, kamar yanda na jima da sadaukar da kaina”. “Miyasa kike da taurin kai Fareedah”. “Shine izzata, ƙarfin gwiwa ta wajen tunkarar maƙiyi na”. Wani irin cije lips yayi daga can, hawayen da tun randa labarin auren wadda ya fara so yake kuma kan so yazo masa da wanda yafi ƙarfinsa suke kwaranya ya kasa sharesu suka shiga rige-rigen zubowa daga idanunsa, yasan ta ƙare kuma, abinda ya rage kawai ƙyautatama masoyiyarsa koda hakan zai kasance sadaukarwa ta ƙarshe da zaiyi a rayuwarsa. “Na barki lafiya, ki kasance cikin aminci da kariyar UBANGIJI”. Ya faɗa harshensa a sarƙe da yanke wayar a lokaci guda. Wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga gudu a fuskar Iffah, bata san tana son Sir Fawzan ba sai a yanzu. A yanzun da kowa zai iya kiransa ƙurarren lokaci a rayuwarta. Zata cigaba da masa fatan alkairin samun madadinta koma wadda ta fita, jin kamar motsin ana tunkaro ɗakin yasata saurin kwanciya taja bargo har saman kanta.... ★★........ “Muhammad Zayyan!”. Kaka ya kira Babiy tamkar yana gabansa cikin matsanancin damuwa da firgici na zahiri dake kan fuskarsa. Ɗago kansa dake sunkuye yay a hankali shima tamkar yana a gaban Kakan. Hakan ya bayyana jajayen idanunsa da damuwa ta rinar. Sun rabu ne tun a wajen ɗaurin aure basu dawo nan gidan ba suka wuce Jumna. “Na'am Baba”. “Kayi haƙuri. Karku zama masu baƙin ciki kai da matarka. Ku zama masu juriya da karɓar ƙaddara rubutacciya daga UBANGIJI. Nasan akwai raɗaɗi, nima kuma makamancin irinsa nakeji a ƙirjina. Sai dai bazan gaji da faɗa maka *_Kibiyar ajali sulke baya tareta sai ta gitta ba_* kamar yanda babu wata duster data isa goge abinda alƙalamin ƙaddara ya rubuta. Mu mun wuce yanzu, dan mungama namu ku ya rage kuyi naku mu barma UBANGIJI sauran, dan dama duka nasa ne. Iyyani itace zata shiryata kafin isowarsu ɗaukarta, nau'in turaren da yake a cikin gidanka kawai nake buƙatar fitar ƙamshinsa daga jikinta. Ta kuma sha iya adadin madara datake gidanka kawai daga yanzun har zuwa wayewar gari. Ta kwana a ɗakin daba shi aka ajiyeta ba. Karta karɓa daga wanda zuciyarta tai rawa a kansa. Ta zama ƴar kallo a takun farko, ta zama kurma a shigar farko, ta zama mai rauni a tawagar farko, tasa a ranta kariyar UBANGIJI na tare da ita. Na barku lafiya”. Ummu ta juya ta kalla Babiy dake riƙe da wayar a hannu tamkar dasashen gunkin da akai ado dashi domin tunawa a tarihi. “Lafiya kuwa? Baba ma baida wata mafita ko? Shiyyasa yaƙi dawowa tanan ya wuce gida?”. Idanu ya cigaba da tsura mata tsahon wasu sakanni harta fara kuka, ya ciza leɓensa na ƙasa yana mai haɗiye abinda ya tokare masa maƙoshi. Gefenta ya kai zaune, tamkar mai bitar karatu ya shiga maimaita kalaman baba a zahiri _“Iyyani za ta shiryata kafin isowarsu ɗaukarta, nau'in turaren da yake a cikin gidanka kawai nake buƙatar fitar ƙamshinsa daga jikinta. Ta kuma sha iya adadin madara datake gidank.......”_ Kallonsa Ummu tai da share hawayenta a lokaci guda, cikin rashin fahimta tace, “Mi kake son faɗa?”. Kansa shima ya girgiza mata. “Ba dagani bane ba, Baba ne. Amma na kasa fahimtar komai Jamaima. Ko ke kin fahimta?”. Har zatace a'a sai kuma tai ɗan jimm idanunta masu girma da su Iffah suka gada a kansa. Itama maimaita kalaman tayi kamar yanda ya faɗa har sau uku, “Idanfa har na fahimta, Baba yana nufin _Iyyani ta shirya Iffah da kanata, idan sunzo da wani turare karmu bari tai amfani da shi, sannan ko taje can an bata wani abu kar taci......, Kaga kenan daga nan mu saka mata turaren, sannan mu bata abinci taci cikinta ya cika. Mu kuma......” Numfashi ya ja daga hancinsa a hankali ya saukar a ƙirjinsa, itama ta sauke numfashin mai haɗe da zubar hawaye sakamakon dakatar da ita da yay da hannu alamar ya fahimta ba sai ta ƙarasa ba. duk da bawai nauyin da zuciyarsa tayi ya ragu bane, ya dai samu sassauci daga kalaman Baba duk da basu san manufarsuba kai tsaye. Sai dai bin umarninsa a garesu tilas ne....... ★ Tsaf Iyyani ta shirya Iffah dake faman zubda hawaye har yanzu cikin shiga ta alfarma kamar yanda Kaka ya bada umarni. Wata haɗaɗɗiyar riga ce da akanga irinta kawai a jikin hamshaƙan matan gidan sarauta na ƙasar ruman mai kama da alƙyabba da ita kanta Iyyani bata taɓa sanin a kwaita a gidansu ba Kaka ya kawo yace a saka mata. Duk da shirine bana daɗin rai ba tayi ƙyau matuƙa. Ga wasu nau'in sirrika na ƙamshi na tashi daga jikinta har suna hawa kai. Tsaff Ummu da kanta ta shirya mata wasu abubuwa masu muhimmanci nata duk da sun san zama ne na taƙaitaccen lokaci ga ƴar tasu mace tilo data rage yanzu. Daga Babiy har Ummu zama sukai suna mata nasiha, nasihar kuma gaba ɗayanta tafi ƙarfine akan addu'a, ta kula da addininta, azkar, karatun alkur'ani kar tai sakaci da su. Babiy da kansa ya ɗakko wayar Fariha ya bata yace ta ɓoye kozasuna rinƙa jinta, baima san ta Arfa ma na hanunta ba. Isowar jama'ar daular ruman ta katse zaman nasu. Inda mayan matan da suka shigo gidan tare da rakkiyar tawagar hadimai suka buƙaci a basu amarya da ruwa mai ɗumi su shiryata. Kan Babiy a ƙasa ya basu amsa da “A shirye take domin cika umarninku”. Sosai mamaki ya bayyana a fuskokinsu dajin kalaman Babiy da kuma fitowar Iffah da Iyyani ta riƙo suka fito. Baki ɗaya daga cikinsu ta buɗe zatai magana wata ta girgiza mata kai alamar kartace komai. Badan taso ba tai shiru, sai dai ta juya ta fita tana mai danna wayar hanunta da alama wani take ƙoƙarin kira. Babiy da kansa ya kama hanun Iffah tare da akwatin kayanta ƙarami har ƙofar gida gaban motar da aka tabbatar masa itace ta ɗaukar amarya.. Da gayya Iffah tai gaba zata kifa suna gab da fita a soron kamar tayi tuntuɓe da rigar jikinta dake jan ƙasa. Da sauri hadimai mazan dake tare da su sukai mata runfa da bayansu dan kar wanda yaganta, dan kofar gidan dama cike yake da jama'a, cikin sauri ta gefenta mai sanye da baƙar abaya harda niƙaf tai ƙoƙarin yin kamar zata tarota suka duƙe tare, a hankali ta ɗan ɗago suka haɗa ido, matar dake ƙoƙarin taimaka mata ɗin tai saurin kautar da nata da sukai jajur tare da ɗaukar littafin da Iffah ta saki ƙasa yayin da take kaiwa sunkuye. Miƙewa matar tai, itama Iffah ta ɗauka envelope ɗin da matar ta saki ƙasa dai-dai Babiy na ɗagota. Da baya-baya Sir Fawzan da yay ɓaddabamin shigar mata cikin baƙar abaya da niƙab kamar hadiman masarauta ya dinga jan jikinsa cikin mutane ƴan kallo har ya sulale gaba ɗaya a wajen..... *_DAULAR RUMAN_* Wannan ne karo na farko da Iffah ta shigo cikin masarautar daular Ruman. Duk da a cikin mota suke kuma har yanzu hawaye basu daina zirara daga idaniyarta zuwa fiskarta ba hakan bai hanata tsarkake sunan UBANGIJI ba, yayin da motocin da suke a ciki suka gama keta katafaren gate ɗin farko zuwa cikin masarautar mai matuƙar girma da hasashe ko kintace bazai iya bayyanawa ba kai tsaye sai al'amarin ya sake girmama zuciyata........✍ Tabɗi jan🙆🏻 Ga aure dai ya ɗauru tsakanin Tajwar Eshaan Bin Haysam Abdull-Majeed. Da Fareedah Bint Zayyan. Shin itama zata mutunne kamar sauran matansa ko zata tsira? Wacece Uwa? Wacece Ta-ƙurya? Wanene shi kansa Tajwar Eshaan da ƴan ƙasar Ruman baki ɗaya kema kallon Fir'aunan wannan ƙarnin?. Miye dalilin mutuwar matan Tajwar? Shike kashesu? Ko akwai lauje cikin naɗi a kashesun?. amsoshinku duk suna a cikakken littafin nan na DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA, dan cakwakiyarfa yanzune ma zata fara😉🤗. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_13_* .........Ta ko'ina bayine masu hidima ga wannan basarakiyar daula. Yo basarakiya mana, dan itace masarauta dake mulkin ƴan ƙasa dama sarakunan ƙasar baki ɗaya. Sun sake wuce gate na biyu inda anan ɗin ma dai katafaren wajene da misaltasa babban aikine ga mai hasashe. Ta ko'ina hadimai ne ke kaiwa da komowa maza da mata. Ga wasu irin gine-gine na alfarma da ɗaukar hankalin mai kallo tamkar ba'a cikin ƙasar Ruman ba. dogayen gine-gine ne da abaya sai dai su hangosu daga nesa tamkar yanda suke iya kallon jirgi yayinda yake keta giza-gizai. Ga wasu irin korayen shukoki tako ina tare da shimfiɗaɗen lafiyayyen titi da za'a iya rantsewa yafi kowanne titi dake a cikin ƙasar Ruman. Kasancewarta farin shiga a ganin wannan shimfiɗaɗɗiyar daula saita fara tunanin anyama kuwa a duniyar mutane take? Kokuwa dai mafarki takeyi ne? Dan sam inda take yafi kama da anguwanin ƙasashen turawan da a tv ne kawai suke iya ganinsu cikin film ko labarai da makamantansu... Har motocin suka samu wajen tsayawa aka fito da ita sam ba'a hayyacinta take ba, bawai ƙawatuwa da tarin ƙyale-ƙyalen da aka zubane kawai ke ɗibar hankalinta ba, akwai wani ɓoyayyen tunani acan ƙasan ruhinta da ƙahon zuciyarta mai alaƙa da tabbatar da abinda mutane ke faɗa akan Daular Ruman ɗin...... Saukar sautin busar sarewa mai zaƙi da daɗin saurare da ya fara tashi a cikin daular Ruman ya sauka cikin kunnenta tare da katse tunaninta ya maidota hayyacinta. Wannan saƙone dake isa zuwa kunnen duk wanda ke a cikin masarautar cewar an iso da _Zawjata almilki_. Tsawon lokaci sautin na tashi har sai da saƙon ya isa ga kunen kowan da ake buƙata. Daga Iffah dai bata san ma'anarsa ba, dan haka bata ɗaukesa komai ba. Sai ma share hawayen fuskarta data cigaba dayi, dan har yanzu fuskar tata na lulluɓe ne da hular ƙawatacciyar rigar jikinta da zamu iya kira alƙyaba. Sai dai zuciyarta cike take da alwashi mai ban tsoro ga duk wanda zai iya jinsa a kunne. Ta sadaukar zata mutu, amma ba ita kaɗai ba harda Shahan-shan na Daular Ruman, idan an hanata damar bayyanama duniya a ƙwato musu ƴancinsu, sai ya mutu aga wanda zai cigaba da kashesu. A karan farko ta saki murmushi mai ƙayatarwa, irin murmushin data jima batayiba kuwa........ Babu wanda ta ɗaga kai ta ko kalla a cikinsu har suka gama bushe-bushen algaitunsu dana sarewa. Cikin girmamawa ɗaya daga cikin matan da suka ɗakkota ta matso gab da ita. “Ran Zawjata-almilki ya daɗe, nan shine sashen Malikat Bushirat. Mahaifiya ga Zakin wannan daula Shahan-shan, Uwa ga duk wani ɗan ƙasar ruman”. A karo na farko Iffah ta ɗan ɗago idanu ta dubeta kaɗan daga cikin alƙyabar, kanta a ƙasa yake ita a dole bazata iya ko haɗa ido da ita ba domin girmamawa. komai batace da ita ba, sai dai ta dubi katafaren ginin da ya tabbatar mata da maganar matar. Idanunta ta maida ta risinar kawai batare data nuna alamar tama jita ba. Abin mamaki bai nema tsaida bugawar zuciyar Iffah ba sai da suka shiga wannan katafaren gini, bayi sai zubewa suke akan gwiyawunsu tamkar wasu masu neman gafara ko kuma Tajwar Eshaan ɗinne da kansa. Zaman faɗa muku daula da dukiyar dake a wannan sashe ma ai ɓata lokacine, dan haka na baku damar ƙiyastama zukatanku kawai.... (Lol😉😋😆) ★Karan farko na tarihi, karan farko na rayuwa, yau ga Iffah gaban *_Malikat Busheerat_*. Mace ta biyu ga tsohon Tajwar Haysam ibn Abdull-Majeed. Mahaifiya ga Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdill-Majeed Shahan-shan na wannan ƙarni. Hamshaƙiyar mace mai tsananin ƙyau tamkar itace ta zaɓama kanta ƙyaƙyƙyawar surar jikinta da zubin halittar ta. A kallo ɗaya da Iffah tai mata daga cikin hular alƙyabar jikinta ta kasa sake ɗaga idanu ta ƙara saboda kwarjininta. Ta tabbatar ta isa a kirata _Malikat_ (Sarauniya), Uwa ga fir'aunan sarki kuma. Kishingiɗe take a ɗaya daga ƙayatattun kujerun katafaren falon daya amsa sunansa daular duniya, wanda kafin isowarsu cikinsa sun wuce manyan faluka da suma suka amsa suna daular duniya bama ta ruman ba kawai. A gefe da gefenta wasu matanne cikin shiga ta alfarma suma har su huɗu, sai hadimai dake zagaye da ita kowanne da hidimar da yake a gareta cikin matsanancin taka tsan-tsan da kai. Dan ko wadda ke tare da ita suna shigowa zubewa ƙasa sukai jikinsu har tsuma yake yi, ita Iffah har tsoroma suka bata tare da mamaki mai girma na wannan ƙarfin iko. Iffah dai na tsaye har sai da ɗaya daga cikin matan nan dake tare da Malikat ta miƙe ta kamota ta zaunar ƙasa bisa lallausan carpet ɗin dake a falon saitin Malikat Bushirat da har yanzu tana a kishingiɗenta kuma ko sau ɗaya bata ɗago ta kalla kowaba tunda suka shigo. Kusan minti biyu falon yay tsitt babu wanda ya sake koda motsin kirki, sai ƙarar na'urar sanyi dake tashi kaɗan-kaɗan da wani ƙamshi na musamman. (To masu karatu inhar Malikat na'a haka, yaya shi kuma Tajwar ɗin zai kasance kenan akan izza da mulki?🤔.) Iffah da shirun ya isheta kaɗan ta ɗago idanunta ta cikin hula ta saci kallonsu. Sai taga su duka har Malikat ɗin ashe ita suka zubama idanu. Haka kawai tasha jinin jikinta, dan kallone bana a santa ba, kallone dake buƙatar nutsuwa kafin a bashi fassara. Kaɗan taja numfashin dake neman maƙale mata a maƙoshi da ƙara yin ƙasa da kanta hular ta sake rufe fuskarta ruff. A hankali, cikin son ɓoye rauninta da hawayen dake neman kwace mata ta furta “Barka da yamma ranki ya daɗe”. “Malikat ta amsa miki, tare da maraba a gareki”. Ɗaya daga cikin matan ta amsa a maimakon Malikat da har yanzu batako motsa daga kishingiɗar da tayi ba. Sai dai ta ɗago ƙyawawan idanunta farare tas ta sake zubasu akan Iffah, idanun ta juya a hankali ta dubi ɗaya daga cikin matan nan dai dake kusa da ita. “An gama ranki ya daɗe”. Matar ta faɗa da girmamawa alamar ta fahimci mi take nufi. Tsam ta miƙe zuwa inda Iffah take, ta kai hannayenta biyu ta kama hular alƙyabbar tai baya da ita, ƙyaƙyƙyawar fuskar Iffah datai jajur saboda kukan da tasha abinka da farar fata ta bayyana. Idanu Iffah ta rumtse sakamakon jin al'amarin a bazata, ga wani irin harbawa da ƙirjinta yayi har sai da ta ambaci (Hasbinallahu wa-ni'imal wakil) a zuciyarta sannan taji numfashinta da yay sama yay ƙasa a lokaci guda ya daidaita. Kaf hadiman ƙasa sukai da kansu, dan haramunne a garesu kallon fuskar *_Zawjata-almilki_* kai tsaye. Yayinda Malikat Bushirat ta motsa a karo na farko daga kishingiɗar da tai idanunta akan Iffah. Kusan kallon mintuna biyu tai mata kafin ta janye idanun cike da ƙasaitar masu isa, yatsun hanunta ta ɗan murza suka bada sautin (ɗass! Ɗass!!!) har sau biyu. Tamkar ƙiftawar ido hadimar dake tsaye riƙe da wani ƙasaitaccen bowl kalar gold da adon stones masu ɗaukar ido ta iso gaban Iffah da kanta ke ƙasa har yanzu tana ambaton ALLAH a zuciyarta ta zube tamkar mai neman gafara. Kanta a ƙasa alamar bazata iya kallon Iffah ba ta miƙa mata bowl ɗin hannu biyu bayan wata a cikin sauran hadiman ta matso da sauri ita kuma ta janye farin ƙyalle da aka yana a saman bowl ɗin tare da murfinsa, tatacciyar madara fara tas ta bayyana. Cikin rawar murya da tsantseni hadimar ta furta, “Ya Zawjata-almilki! Wannan madara ce mai daraja daga hannun Malikat domin nuna maraba da zuwa a gareki cikin DAULAR RUMAN”. Shiru Iffah bata da alamar motsawa, har hakan ya bama duk wanda ke gurin mamaki har Malikat Bushirat. Tsahon sakanni goma kafin ta ɗago. Manyan idanunta da sukaci kuka har suka gode ALLAH ta zubama bowl ɗin tare da hadimar dake gurfane a gabanta tamkar mai neman gafara. Kanta ta girgiza a hankali tare da sake maidashi ta risinar. Cikin motsa laɓɓanta a hankali tace, “Wannan karamci abin alfaharine a gareni da nuna tsantsar godiya ga Uwa gareni dama ƙasar Ruman baki ɗaya. Sai dai ina mai neman afuwar jinkirtamin shan wannan madara sakamakon azumtar wannan yini da nakeyi batare da nasan yau zata kasance rana mafi daraja da alfarma a gareni ba”. Kalaman Iffah da tasirinsu tamkar saƙar ƙudan zumace cikin kuttu a zukatan duk wani mai numfashi dake a wannan falo. A zahiri da baɗini kuma babu wanda mamaki bai bayyana akan fuskarsa ba, saboda abune da bai taɓa faruwaba a cikin daular ruman. Malikat Bushirat tai ƙyauta a jinkirta amsa tare da biyo jinkirin da sharhin da babu gargada akan harshen mai furtashi. Wannan abu yakai a kalla Iffah a sake kallonta dan ko ƴaƴan gidajen sarauta goma cif da aka kawo daular a irin matsayinta basu samu ƙwarin gwiwar ƙin shan irin wannan madara ba. Hasalima kowaccensu da rawar jiki take amsa ta shanye tas ta bada bowl ɗin tana mai gurfana a gaban Malikat domin yin godiya. Ba'a matsayi kuma kawai ba hatta a shekaru Iffah itace mafi ƙanƙanta a cikin Zawjata-almilki goma sha huɗu da aka kawo gidan. Ɗaya daga cikin matance ta zabura idanunta dake nuna ɓacin rai akan Iffah. Sai dai abin mamaki Malikat Bushirat da idanunta ke kan Iffah ko ƙyaftawa babu ta ɗaga mata hannu alamar ta zauna tare da sakin wani ƙasaitaccen murmushi. Nuni tai akan a rufe madarar. Ruf aka maidata yanda take hadimar ta miƙe daga gaban Iffah da tunda ta sake maida kanta ta rissinar bata ƙara ko motsawa ba. A karo na farko Malikat ta motsa laɓɓanta, cike da izza da ƙasaita irin ta manyan masu mulki. “A kaita masaukinta”. Ƙasaitacciyar muryarta ta ratsa zuciyar Iffah tare da girgiza gaɓɓanta cikin ikon harbawar jini. Sunan ALLAH ta ƙara tsarkakewa a zuciyarta dan tabbas Malikat ta cika Malikat ɗin babu tantama. Saboda muryar tata kanta barazanace ga duk mai yunƙurin kawoma girmanta wargi da saka tsantseni a zuciyar duk wani talaka dake a ƙarƙashin mulkinta. “Ki huta lafiya, cikin aminci da farin ciki”. Iffah ta faɗa cikin risinar da kanta alamar girmamawa lokacin da take miƙewa bisa taimakon ɗaya daga cikin matan nan. Yin hakan ya sake saka zukatansu a mamaki, ita kanta Malikat Bushirat da kallon ƙasan ido ta bisu har suka fice. A ƙasan ranta tana mai jin farin cikin samuwar Zawjata-almilki data dace da gudan jininta tilo kuma Shahan-shan na ƙasar Ruman gaba ɗaya. A ganinta lokacine daya dace tai yaƙi da maƙiyanta masu yaƙar Zakinta a yanzu dake zagaye da su..... ★★Kamar yanda Malikat Bushirat ta bada umarni amarya Iffah (Zawjata-almilki) an isa da ita sashenta dake gab da sashen matan Tajwar Eshaan su biyu da har yau suke raye, sannan kuma kusa da katafaren sashen Tajwar Eshaan da yafi kowanne gini ɗaukar hankali da kayan kyale-ƙyale da tsagwaren dukiya a cikin Daular Ruman harma da tsantsar tsaro... Sashen Iffah ya kasance shima sashe dake ɗauke da nau'in kayan more rayuwa da a kallo ɗaya mai karatu zai tabbatar da sai dai Zawjata-almilki ɗince kawai kam ta dace da zama a cikinsa. Kamar yanda al'adar take anyi rakkiyar Iffah dake kan keken doki tare da busar sarewa mai daɗin saurare har zuwa sashen nata. Iya masu hurumin shiga kawai suka shiga har cikin bedroom da suka kira matsayin master bedroom nata. Sai dai suna fita ta miƙe daga zaman ɗofanar da tai a gefen gadon, cikin ambaton sunan ALLAH da zubar hawaye ta jaye hular alƙyabar ta ta ƙarema ɗakin kallo na tsahon mintuna uku. Komai batace ba ta ɗauka akwatinta da aka shigo da shi ta fito a ɗakin tare da jawo ƙofar. Bata wani tsaya kallon falon data fito ba, sai dai tabi kowace kusurwa na cikinsa domin lissafa adadin ƙofofin dake a cikin. Ƙofar da lissafinta ya tabbatar mata ta nufa, cikin ɗan jimami da tausayin kai ta murɗa ƙofar mai kalar ruwan gold. Ɗakin ta shiga bayan ta leƙa kanta cikinsa. Shima ɗin dai a ƙayace yake da komai na alfarma. Sai dai komai nasa ya banbanta da kalar na wancan ɗakin. Amma shima duk abinda ke cikinsa royal ne irin kayan da suka dace da gidan hamshaƙan masarautu kamar Daular Ruman. Ajiyar zuciya ta sauke bata samun nutsuwa ba, sai ta son rage nauyi mai danƙarewa a ƙirji kawai har numfashi ya gaza samun damar fita yanda ake buƙata. Jikkar ta ajiye tare da zama bakin gadon ta rushe da sabon kuka.........✍ _To ko burin Malikat Bushirat zai cika kuwa? Kokuwa dai itama Iffah zata suɓucema ƙwarin gwiwar tata tamkar Zawjata-almilki na baya da suka shuɗe ta hanyar kisan da har yanzu ba'a san wanene sanadinsa ba?. Idan Shahan-shan ne da kansa yaya Malikat zata kasance a wannan yaƙin kenan? Dan masu iya magana kance fa DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA.._ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_14_* .........Wannan dare darene na tarihin da har abadan Iffah bazata taɓa mantawa da shi ba. Badan wani abu ya faru bayan wanda ya faruba, wanda ya farunne bazai taɓa zama shiɗaɗɗe a zuciyarta ba. Kwana ɗaya tak ta kasance cikin ɗimuwa da tsananin kewar ahalinta. Wanda ta riga ta gama sallamawa ta rabu dasu kenan har gaban abada. Sai dai bayan mutuwarta suzo jana'izarta batare da ko kan gawarta an barsu matsawa ba. Sam babu wani barci koda ɓarawo da yaci galabar ɗaukarta a wannan dare. Hakama abincin da aka biyo bayanta da shi na buɗa bakin azumin da tace batacisa ba. Kuka taci ta ƙoshi har kusan rabawar dare kafin ta miƙe zuwa bayi tayo alwala ta nutsu gaba ɗayanta gaban UBANGIJIN talikai maji roƙon bayinsa. Duk da tsananin tsoro da take a ciki na kasancewa ita kaɗai a katafaren sashen haka ta dinga jarumtar son dannewa a zahiri. Sai dai duk ƙanƙantar motsi yakan saka zuciyarta harbawa da tunanin anzo kashetane. Tana idar da sallar asubahi barci yafa ce ya shirya, dan duk yanda take faman turesa da son ƙin yinsa sai da yakaita ƙasa, dole takai kwance kan lafiyayyen kafet ɗin dake gaban gadon kafin ƙiftawar ido ta fara sauke numfashi.... Barci sosai Iffah tasha na tsahon lokaci mai tsayi da har sai da aka tadata ta fahimci hakan. Ƙyawawan idanunta dake cike da barci ta buɗe da ƙyar akan matar dake tsaye a gabanta kanta a rissine. Babbar mace ce mai shekaru sosai, sai dai shigarta ta tabbatar da cewa ita ɗin bakomai bace sai hadima a masarautar. Amma kuma da alama hadima ce mai babban muƙami da matsayi.... “Barka da safiya ya Zawjata-almilki”. Ta katse tunanin Iffah ta hanyar gaisheta. Yunƙurawa tai ta tashi zaune idonta na a kanta, kanta ta gyaɗa da faɗin, “Mama ina kwana”. Dan shekarun girma na matar ya wuce ta zauna saita gaisheta. Sosai ta ga ruɗewa da kiɗima a idanun matar. Cikin yin waige-waige na tsoron kar wani yaji ta zube ƙasa da rawar harshe. “Ranki ya daɗe na roƙeki dan ALLAH wannan sunan yabar fita a bakinki. Kece uwa a garemu, ke kika cancanta mu kira da sunan bani ƙasƙantacciyar baiwa mai miki hidima ba. Sunana shine Diwa, zaki iya kiran Ama (baiwa), ni shugabar hadimai masu kula da tsaftar sashen Malikat ce. An kawo miki abin karin kumallone tare da wanda zasu shiryaki da hadiman da zasu kasance masu hidima a gareki”. Idanu kawai Iffah ta tsura mata cike da tausayawa. Sai dai komai bata iya cewa ba ta kauda idanunta zuciyarta na ƙuna na raɗaɗin ƙasƙancin da su talakawan ruman ke fuskanta a ƙarƙashin waɗannan masarautu. Hadima Diwa miƙewa tai da sauri ta fita. Mintuna kaɗan sai gata ta dawo tare da wasu mata guda biyu. “Ranki ya daɗe, waɗannan matan sune zasu shiryaki a yanzu”. Yanzun ma iyakarta ɗago ido ta kallesu kawai, sai dai batayi musu ba wajen basu damar fara aikinsu. Amma a zuciyarta ta cigaba da yin addu'a sakamakon harbawa da ƙirjinta keyi da sauri-sauri tamkar mai tsoron tunkarar wani abu. Tsaf suka kwance kitson dake kanta, dogon gashinta da mafi yawan ƴan ƙasar ta Ruman keda ya bayyana. “ALLAH ya ƙara miƙi tsahon rai da lafiya, wannan lokacine na wanka”. Komai Iffah batace musu ba ta miƙe, dan tanabin huɗubar Kaka ne daki-daki. Da zata shiga bayi dakatar da su tai daga ƙoƙarin binta da suke. Hadima Diwa dake gurfane gefe tai saurin faɗin, “Ranki ya daɗe ki basu dama dan ALLAH, dan zasu nuna miki yanda zaki amfani da kayan wankan da aka shirya dominki a ciki, su kuma gyara miki kai kawai su fito”. “Karki damu zanyi da kaina”. Ta faɗa tana mai shigewa kafin ma ta sake cewa wani abu, sai dai bakinta ɗauke yake da addu'a. Wani irin harbawa zuciyarta tayi, tareda sarawar kai lokacin da take sanya ƙafa cikin toilet ɗin sai kace ba dashi tai amfani ba da asubahi, yanzu kuma da su Diwa suka shikago sun gyarasa da ajiye kayan wankan da suka shigo da shi tare da matan, hannu takai saman kanta tana karanto addu'a bayan ta shiga toilet da tayi sannan ta ƙarasa shiga. Shi kansa bayin abin kallone a yanzu fiye da ɗazun, dan yanzu an ƙawatashine da wasu irin fure da candles ta gefen jakuzzie ɗin. Sai wasu nau'inkan ruwan turare da aka ajiye domin tai amfani da shi, sam zuciyarta taƙi aminta da hakan, atake ta dinga ɗaga tasoshin da suke a ciki tana maidasu gefe guda ta hau wankanta tana mai zubda hawayen tausayin kanta dana iyayenta da batasan halin da suke ba a yanzun suma.... Koda ta fito da tunanin samun matan data bari sai taci karo da akasin haka. Domin kuwa wayam ɗakin babu kowa, sai ƙamshi mai daɗi na turaren wuta da aka ajiye ke tashi. Numfashi ta sauke a hankali, badan samun nutsuwa na abinda ke gudana ba. Sai dan samun sassaucin nauyin da zuciyarta tai mata. Kusan mintuna biyar da fitowarta ta gagara tsinana komai, hasalima bata san ta ina zata fara ba. Knocking ƙofar da neman izinin shigowa ya sakata ɗaga idanunta manya takai dubanta, kafin ta bada izinin shigowa tana mai janye idanun nata. Hadima Diwa ta shigo sallama kanta a ƙasa, tun'a bakin ƙofa ta zube bisa gwiyawunta. Cike da tsantseni irin na tsakanin yaro da uban gidansa murya cike da rauni tace, “Ya Zawjata-almilki! Yanzu lokacine na shiryawarki da taimakon waɗan nan mata”. Ta ƙare maganar da nuna bayanta. Iffah dake saurarenta tare da zuba mata ido kallonta ta kai bayan nata, kamar zatai magana sai kuma ta fasa. Tai ɗan shiru na wasu sakanni tamkar mai tunani kafin taja numfashi. “Ai zan iya shirya kaina su barshi kawai”. Ƙasa Diwa ta sake yi da kanta da sake gurfana ƙasa sosai. “Ki gafarceni ya Zawjata-almilki. An basu umarnine, saɓawa kuma a garesu tamkar bijirewa ne?”. Tsantsar tausayinsu da takaici mai gimtse maƙoshi ya sake baibaye Iffah, ta nisa tare da haɗiye abinda ya tokare ƙirjinta tana mai jin-jina kai wa hadima Diwa kawai. Tamkar ƙyaftawar ido matan suka shigo su biyu. Suma dai kallonsu kawai Iffah take cike da tausaya wa. dan cike da girmamawa a gareta suka zube gwiyawunsu a ƙasa domin gaisuwa a gareta kasancewar bana ɗazun bane. “Dan ALLAH ku miƙe”. Ta faɗa cikin wani irin yanayi daya saka matan ɗan ɗagowa suka dubeta. Su ɗin ababen tausayine, amma sai sukaji itace suke tausayi fiye da kansu. Umarninta sukabi duk suka miƙe ɗin, suna maiji da kallonta da matuƙar girma a idanunsu duk da ƙanƙantar ta, dan kuwa itace mafi ƙarancin girma a cikin Zawjata-almilki da aka kawo daular ruman. Sun mata shiri irin na Zawjata-almilki data isa a kirata da wannan sunan. Dan ƙwalliyar tata ta dace da halittar ƙyaƙyƙyawar surar jikinta da ƙyawunta. Ta cancanci a kirata Malikat Fareedah bayan Zawjata-almilki duk da ƙanƙantar shekarunta. Saboda duk da damuwar dake shimfiɗe a ƙyaƙyƙyawar fuskarta hakan bai hana bayyanar fitar kwalliyar ƙawata kwarjininta da cikar haiba ba. Su kansu hadiman dake zagaye da ita sai faman satar kallonta suke. Bawai dan tafi duk sauran Zawjata-almilki da suka shuɗe ƙyawu ba, kawai natan ya matuƙar ƙayatar dasu ne batare da sun san dalili ba. Ita a karan kanta kallon kanta take dajin tamkar ba ita ɗin bace, bawai dan ƙyale-ƙyalen gold da diamonds da aka ƙawata adon jikin nata da shi ba. Hasalima sune abu na farko da takejin tsantsenin gani a jikinta. Hadima Diwa data sake neman izinin shigowa ta shigo a gabanta ta sake zubewa tana mai satar kallonta itama. Cikin jinjina girma irin na UBANGIJI mai halittar abinda yaso a yanda yaso ta isar da saƙonta kamar haka.... “Ya Zawjata-almilki! Yanzu shine lokacin karin kumallonki”. Iffah da takurar ta fara gundurarta ta saurin tarar numfashinta, “Bana buƙatar cin komai nikam Mama”. Tamkar hadima Diwa zatai kuka, muryarta har rawa take wajen faɗin, “Ki gafarceni ranki ya daɗe. Wannan suna bai dace da niba, jinsa a harshenki zai tabbatar da hukunci mai tsanani a gareni. Hakama rashin cin abincinki a yanzu”. (Ya rabba). Iffah ta ambata a zuciyarta cike da takaici dajin sake tsanar Tajwar Eshaan dama duk mai faɗa aji na masarautar. Bata sake magana ba ta miƙe suka fito da hadima Diwa. Dan matan da suka mata kwalliya tuni sun fice su. Babu kowa a ƙaramin falon da Diwa tai mata jagora, inda aka shirya abinci kala-kala kai kace su goma zasu cisa. Ita a rantama tunani tai ko tare da Tajwar Eshaan ɗinne ma. Sai da taga har takai zaune Diwa na ƙoƙarin fara haɗa mata abincin ta tabbatar domin ita kawai akayi kenan. Komai batace ba, har Diwa ta gama buɗe abincin duka alamar taga wanda take buƙata kenan. Komai kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kanta, da ga ƙarshe ta nuna mata dafaffiyar madara kaɗai. Diwa tai jimm kamar mai tunani, sai kuma ta saci kallon Iffah ɗin tai saurin maida kanta ƙasa. Iffah da duk ke kallonta ta ƙasan ido ta cigaba da nazarinta harta kammala zuba mata madarar. Gabanta tazo ta ajiye, harta yunƙura zata miƙe ta dakatar da ita. “Bani zan sha ba ai mama naki ne”. A wani irin matuƙar hargitse Diwa ta ɗago tana duban ta, jikinta har wani karkarwa yake. “R....ran...ki ya daɗe w...w..wan nan ai ba hurumina bane”. Iffah data kafeta da idanu ko ƙyaftawa batayi ta janyesu a hankali tana mai miƙewa abinta batare da tace komai ba. Da sauri Diwa ta ƙara gurfana a gabanta tana hurwa. “Ranki ya daɗe dan ALLAH karkice bazakici komai ba, dan komai anan umarnine”. Bata zauna ɗin ba, ba kuma tace komai ba. Sai ma ɗakin da suka fito data nufa zuciyarta cike da nauyi. Batafi zaman mintuna biyarba wasu mata da batako musu kallo biyu ba suka iso da wata hamshaƙiyar riga mai kamar alƙyabba daga Malikat. Tare da umarnin tafiya da ita. Batai musu ba, dan a nata tunanin Malikat Bushirat suke nufi, sai dai zuciyarta ta kasa nutsuwa. Addu'a ta shiga ambato a zuciyarta har suka kammala saka mata ƙawatacciyar rigar alƙyabar mai tsananin ado da ɗaukar idanu, zasu kunna mata turaren wuta da suka shigo da shi a burner tai saurin dakatar da su. Kallon juna sukai, kafin ɗaya tai saurin faɗin cikin ƙanƙan da kai, “Ya Zawjata-almilki wannan umarnine daga Malikat”. Yamutsa fuska Iffah tai tana mai kallonta, kallo irin na wannan bata san wacece autar Babiy ba ta ɗauke kai. A karon farko tun shigowarta gidan tai magana da harshen ƙarfin zuciya ta ajiye rauninta a gefe. “Ni kuma wannan umarnina ne bana buƙata. Sai kumuje umarni na gaba”. Babu wanda a cikinsu baiji yayi sumar wucin gadi ba. Sai dai wani irin kwarjininta da jin shakkarta ya gama ɗarsuwa a zukatansu lokaci guda.. Iffah dake jin jininta na wani irin tsitstsinkewa ta sake dubansu da niyyar magana, tamkar wadda aka jefa da narkakken ƙarfe taji yafff! A ƙirjinta. Da sauri ta dafe ƙirjin tana mai rumtse idanunta. Rawar da jikinta ya farayi ya sata zubewa ƙasa tana mai ƙoƙarin ambaton sunan ALLAH, amma hakan ya gagara, dan tamkar an naɗe zuciyartane da harshenta a lokaci guda...... Har rige-rigen fita hadiman nan sukeyi jikinsu na matuƙar rawa. Diwa dake zaune a falo tana jiran fitowarsu ta miƙe da sauri tana tambayar lafiya? Babu wanda ya saurareta a cikinsu suka fice. Hankalintane ya tashi, tai kamar zata bisu sai kuma ta fasa ta nufi ɗakin da Iffah take. Wani irin mugun bugawa ƙirjinta yay damm. Innalillahi..... ta shiga ambata dayin kan Iffah dake ta faman juye-juye a ƙasa, cikin ƙanƙanin lokaci ta jiƙe sharkaf da zufa tamkar an watsa mata ruwa koma an tsamota a ciki. Harta kusa kai hannu kanta sai kuma taja baya da sauri cikin tsoro. Ina bai kamataba, matsayinta na hadima hanunta ya taɓa Zawjata-almilki. A daburce tai waje da nufin isar da saƙo ga Malikat Bushirat duk da bata da tabbacin samun iso cikin sauƙi........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_16_* ........Cikin ƙanƙanin lokaci labarin abinda ke faruwa da Zawjata-almilki ta uku ya gama gauraye daular ruman. A take ko'ina yay tsit sai ƙus-ƙus da maganar ido kawai. Sauran Zawjata-almilki kuwa guda biyu dake gidan dama kafin kawo Iffah tuni sun sake shiga tsantsar tashin hankalin da yafi wanda suke ciki. Su dai dama rayuwa suke cikin jiran tsammanin isowar mutuwarsu. Ko lokacin da aka sanar musu sake ɗaura auren Tajwar da wata matar tsantsar tausayin kansune kawai ya baibayesu, yanzu kam jin halin da matar da aka kawo jiya take ciki ya tabbatar musu suma mutuwarsu tunkarosu take sakeyi kenan....... Duk wata tuhumar data dace akan hadima Jaza da sauran hadimai biyu da sukaje ɗakin Iffah suma da aka gano anyi amma sunƙi faɗar gaskiyar wanda ya sakasu, sai cewa suke Diwa ce. Yayinda Diwa ke rantsuwa da ALLAH tana kuka akan ƙarya suke mata ita bata san komai ba. Iya jigatuwa sun jigatu har takai numfashi da ƙyar sukeyi saboda azabartawar da ake musu. Sanin rayuwarsu akafi buƙata a yanzu sama da mutuwarsu yasa hadiman kurkukun dake a cikin daular ruman tsagaita musu. Amintaccen hadimin Malikat Bushirat ya koma ya sanar mata halin da ake ciki. Shiru kamar bazatace komaiba. Sai kuma ta dubi Jasrah da har yanzu ke tare da ita ta ɗauke kanta. Jasrah data fahimci mi ƴar uwar tata ke nufi takai dubanta ga hadimin. “Ghazi! A cigaba da tsaurara musu tsaro har zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu”. “ALLAH ya ƙara miki lafiya an gama”. Ya faɗa da tsantsar girmamawa yana mai rissinawa da gyara takobin hanunsa ya fice....... *_ZAWJATA-ALMILKI_* Tun Iffah na iya motsa jikinta da furta kalmar bakinta har hakan ya gagara numfashinta ya fara neman barin jikinta. Ga dai masu magani mata rufe a kanta mazan na daga waje suna haɗo duk abinda ya dace amma babu alamar wani canji sai ma ƙwaɓewa da komai ke nemanyi. Tun ana ƙirga awannin iya shawo kan matsalar har komai ya fara firgita kowa. Daular ruman tayi tsitt babu mai ƙwaƙwaran motsi a cikinta. Sautin fitar kiran salla ma dan ya zama dolene. Koda aka idar da salla ma sake komawa zaman jigum-jigum akayi domin kuwa abinda bai taɓa faruwa a tarihin masarautar bane ya faru. Tajwar Eshaan bai fito sallar zuhur ba yau. Hakama da la'asar. Magrib ma ta shiga babu wanda yaji motsinsa. Zuwa lokacin kuma akan Iffah an zubama sarautar ALLAH idone wadda ta girma ta ɗaukaka. Dan kuwa tana a shimfiɗene jiki duk ya ɗashe tamkar wadda ta ƙone gurin yay ja kafin ya tashi. Kaɗan-kaɗan numfashinta ke fita wanda shine kawai ya tabbatar da tana a raye bata mutu ba. Masu magani kowa yayi iya iyawarsa sun koma gefe ana jiran ikon ALLAH kuma. Ana idar da sallar la'asar Malikat Bushirat ta bada izinin maida Iffah sashenta..... Kamar yanda Malikat Bushirat ta bada umarni an maida Iffah sashenta, a kuma cikin ɗakin barcinta da babu wani mahaluki daya taɓa shiga bayan Tajwar Eshaan da Jasrah. Hakan ya bama dukkan hadiman sashen mamaki da tabbatar da lallai wannan Zawjata-almilki ɗin tana da wata daraja ta musamman ga Malikat. Dan kaf Zawjata-almilki da suka rasa rayuwukansu a gidan babu wanda ya iya ganin makamancin damuwar Malikat Bushirat irin ta yau. Ƙarin tabbaci har hawaye sai da ta share na tsagwaron tausayin Iffah. Lallai halin da Iffah ke ciki ta cancanci duk mai imani ya zubda mata hawaye, dan sauran Zawjata-almilki na baya mutuwarsu kawai akeji bayan kaisu turakarsa. Amma ita ko kaitanma ba'ayiba, a kwana ɗaya tak da tai a gidan batare da an kammala gagarumin taron bikin da aka shirya ba dominta gata a halin da gara mutuwa da shi... Bayan idar da sallar isha'i Malikat Bushirat na hakimce a katafaren falonta na uku Malikat Ashwaq ta iso da tawagar hadimanta duba Iffah. Malikat Ashwaq itace mace ta farko ga marigayi Tajwar Haysam ibn Abdull-majeed. Hamshaƙiyar mace ce data isa take kuma amsa suna Malikat. A ƙa'idar Daular ruman matar data haifi yarima mai jiran gado a cikin matan sarkice kawai ake kira da Malikat. Mafi yawanci kuma ana samu ne daga matan farko. Sai dai ga Tajwar Haysam hakan bata faru ba. Dan matarsa ta farko Ameera Ashwaq bata taɓa haihuwa ba kamar sauran matansa, tadai taɓa ɓarin ciki na wata huɗu daga shi kuma bata ƙara ba. A zahiri mace ce isashiya mai baza mulkin da yafi na kowace mace a gidan bayan malikat Bushirat, amma kuma bata da damuwa sam. Ƙaryarka kace ga wani mugun halinta na zahiri saboda tasan kanta. Rana ɗaya aka ɗaura aurenta dana Malikat Bushirat matsayin Zawjata-almilki. Amma itace uwargida. Duk da mulkinta Malikat Bushirat ta fita, ta kuma fita zafi da nuna kishi a zahiri dan sam ita bata da haƙuri, hakan yasa ake matuƙar jin tsoronta fiye da kowace Zawjata-almilki, dan Malikat Bushirat ba kanwar lasa bace ƙwarai da gaske, sai dai mace ce mai son ƙyautatama wanda yay mata da na ƙasa da ita, hakan ya taimaka mata samun soyayyar hadiman gidan. Haihuwar Miran (Yarima) mai jiran gado Eshaan tasa dole sunan Malikat ya koma kan Malikat Bushirat. Wato Sarauniya Bushirat kenan. Amma duk da haka sai Mahaifiyar Tajwar Haysam mai suna Malikat Haseena ta bada umarnin cigaba da kiran Ashwaq da suna Malikat Ashwaq. Hakan ya ƙona ran Malikat Bushirat, sai dai babu yanda zatayi. Amma ta sake tsananta kishin da takema Malikat Ashwaq ɗin fiye da da, yayinda ita kuma Malikat Ashwaq ke nuna tamkar babu komai a zahiri, amma a baɗini hummm.... Koda ta shigo Malikat Bushirat bata nuna tasan da shigowar tata ba. Sai dai ta ɗagama hadimanta yatsu biyu da ya sakasu rige-rigen fara barin falon. Zaune Malikat Ashwaq takai bisa ɗaya daga cikin kujerun falon tanama nata hadiman nuni dasu fita suma. Da sauri suma duk suka fice aka barsu su biyu kawai. A hankali Malikat Ashwaq ta ɗan sakin murmushi daya danne zafin yarfin da Malikat Bushirat ɗin tai mata, ita ta fara gaisheta da tambayar ya mai jiki?. A daƙile Malikat Bishirat da tai kamar zata basar ta amsa mata cike da isa. Nanma Malikat Ashwaq dai murmushi kawai tayi da haɗiye ɓacin ranta. Sosai ta nuna tausayi akan Iffah ta kuma mata doguwar addu'a da bada shawarar mizai hana a kira likita ma ya duba ta ko wani abune daban da wanda ake tunani. Karan farko Malikat Bushirat ta ɗakko manyan idanunta tai mata kallon tsakkiyar ido. Cikin yamutsa fuska taja numfashi da fesarwa, “Haihuwar magajin Daular ruman daga tsatson Malikat Bushirat rubutacciyar ƙaddara ce da duk yaƙi da gwagwarmayar masu son daƙile hakan. A baya basuci nasara ba, Taya suke tunanin samunta a yanzu kan _Saifulmulk_ ɗi na?. Kamar yanda aka haifesa daga matsayin gudan jinin Shahan-shan, Tajwar Haysam ibn Abdul-majeed. Shima haka za'a samar da Ɗa daga gudan jininsa da izinin UBANGIJI masu lissafi su fara...” Muƙutt Malikat Ashwaq ta haɗiye yawun dake neman kufce mata, a zahiri kuwa murmushi ta saki da ɗan girgiza kanta. Batare da tace komai ba tai yunƙurin miƙewa domin barin ɗakin tana mai ƙoƙarin danne zuciyarta dake yunƙurowa. Har tayi taku biyu sai kuma ta tsaya, batare data juyi ba ta saki murmushi. “Idan dai har Eshaan ya kasance gudan jinin Shahan-shan ne babu gauraye, muma irin wannan fatanne a bakunanmu garesa kasancewarmu uwaye a wajensa. Fatan alkairi da samuwar lafiya ga Zawjata-almilki.....” Har tsakkiyar kai kalaman ƙarshe na Malikat Ashwaq suka daki zuciyar Malikat Bushirat, sai dai kafin ta samu wani damar fassarasu sallamar Ameera Danish-Ara da suka kusan kiciɓus da Malikat Ashwaq ya dakatar da ita. Itace mata ta uku ga Tajwar Haysam. itama da tata tawagar hadiman. Kallon juna sukai da Malikat Ashwaq, Ameera Danish-Ara ta saki wani malalacin murmushi a kaikaice. Sai kuma ta matso cikin girmamawa ta gaishe da Malikat Ashwaq ɗin datai mata kallo guda ta ɗauke kanta. Amsa mata tai cike da ƙasaita, kafin ta matsa ta bata hanya ta shige, itama ta fice tawagarta biye da ita. Saɓanin Malikat Ashwaq ita ta samu tarba daga malikat Bushirat. Dan duk da take mata itama ga Tajwar kuma Malikat Bushirat kishiya a gareta hakan bai hanata risinawa ta gaidata ba da matuƙar girmamawa tana mai tambayar jikin Iffah. Malikat Bushirat dake kishingiɗe har yanzu a yanda Malikat Ashwaq ta barta ta amsa mata da sassauci mai haɗe da jimami. Cike da makirci Ameera Danish-Ara ke nuna tsantsar tausayin Iffah tana mai yin ALLAH wadai ga duk mai hannu akan waɗan nan al'amura. Malikat Bushirat taɗan jinjina kai irin na ƙasaitattun mata da yamutsa fuska kaɗan, a saman lips ta furta, “Nagode”. A kaikaice Amera Danish-Ara ta ɗan saƙi murmushi tare da harararta ta ƙasan ido. A zahiri kuwa zamanta ta gyara tare da risinar da kanta. “Wannan abunda ya shafemune ai gaba ɗaya ranki ya daɗe. Domin Zaki ɗammu ne, fatammu dai ALLAH ya warware waɗannan al'amura cikin sauƙi”. Har cikin zuciya Malikat Bushirat taji daɗin kalaman Amera Danish-Ara, dan haka a lips ta amsa da “amin” tana mai sauke ajiyar zuciya, dan bata cika samun damuwa da ita a gidanba tunma sunada ƙuruciya. Amera Danish-Ara mace ce mai tsananin kissa da ba lallai a lokaci guda ka iya gano wacece ita ba. Duk da kasancewar ita Zawjata-almilki ce a daular ruman zakasha mamakin irin girman da take bama Malikat Ashwaq da Malikat Bushirat a gidan a zahiri tunda ta shigo. Kai hatta da Amera Haifah dake amarya kuma ƙarama a cikinsu ita bata taɓa bari saɓani ya shiga tsakaninsu ba a zahiri. Wannan halin nata yasa sanda surukarsu Malikat Haseena ke da lafiyar ƙafa take sonta da janta a jiki fiye da su Malikat Bushirat. Wani lokacin har kwatance take musu da halin Amera Danish-Ara ɗin wai suyi koyi ta fisu dattako. A yanzu haka da take zaune babu lafiyar ƙafa Ameera Danish-Ara ɗin tafi kowa sintirin zuwa dubata da mata hidima a zahirance, duk da itama Malikat Bushirat na kamantawa sai dai babu ruwanta da sai wani ya gani yace tayi. Shiru falon ya ɗauka na wasu mintuna, Amera Danish-Ara na son taga Iffah babu fuska ga Malikat Bushirat, dole ta miƙe cikin ƴan kame-kame tana tambayar ko Amera Haifah tazo kuwa?. Kallon ƙasan ido Malikat Bushirat tai mata tana ƙara tsuke fuska, dan ita duk yanda take da zafi babu wanda zaice ga ranar data zauna maganar wani a cikinsu koda da su Jasrah ne kuwa. A ganinta idan tai hakan sunma isa kenan a wajenta. Murmushin yaƙe Amera Danish-Ara tayi cike da basarwa. Sai dai ƙasƙantaccen kallon da Malikat Bushirat tai mata ya matuƙar sokar mata zuciya. Taɗan risina da faɗin, “Na barki lafiya ranki ya daɗe”. Kai kawai Malikat Bushirat ta jinjina mata batare data ko ɗago ba. Amera Danish-Ara ta cije baki da ficewa hadimanta dake jiranta daga falo na biyu suka take mata baya. Sam Amera Danish-Ara bata gaban Malikat Bushirat, kalaman Malikat Ashwaq ne keta faman mata kaikawo a zuciya musamman na ƙarshe. (Fatan alkairi da samuwar lafiya ga Zawjata-almilki) waɗan kalamai bakwai a cikin tarin kalaman Malikat Ashwaq sunfi komi tsayawa Malikat Bushirat a zuciya. Dan kuwa tana fassarasu ne da wani abu daban ne. Haka manyan mutanen masarautar suka cigaba da shigowa duba Iffah daga sassa daban-daban na gidan. wasu iyaye ne, wasu yayu, wasu ƴaƴa harma da kakanni maza da mata duk da basu samun damar shiga ciki iyakarsu wajen Malikat Bushirat. Bata damu kanta ba sai da dare yaja. Koda hadimanta suka dawo sallamarsu tai dan tafi buƙatar kaɗaici a yanzu saboda son ƙara tunani akan kalaman Malikat Ashwaq da suka gagara haɗiyuwa a gareta. Da kuma nazartar kowa daya shigo sashen nata domin duba Iffah. Tun tana a zaune har takai ta miƙe tsaye hannayenta goye da bayanta tana faman kaikawo tamkar mai safa da marwa..........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_17_* ...........Dare yayi nisa, bakajin motsin kowa a daular ruman sai sassanyar iskar dake kaɗa bishiyoyi kaɗan-kaɗan. Sai kuma Hadiman da ake kira Ghazi a masarautar ne kawai ke faman kaikawo domin bada tsaro ta kowacce kusurwa ta gidan musamman a sashen Tajwar Eshaan. Iffah dake kwance samɓal a katafaran gadon alfarma na Malikat Bushirat idanunta a rufe kai kace batama numfashine ta fara zabura a hankali kamar wadda ake mintsini. Jasrah ce kawai tare da ita a ɗakin, tana daga gefe barci ya ɗan figeta mai cike da wani irin mummunan mafarki. Wata gigitacciyar ƙara da Iffah ta fassa tare da girgizar data saka gadon shima rinƙa girgizawa yasa Jasrah farkawa a kiɗime. Tsalle tai gefe jikinta na rawa ganin yanda Iffah da gadon ke girgiza, hatta shi kansa ɗakin ji Jasrah keyi na mata rawa shida fitulun da suka haskesa, dan sai daukewa suke suna kawowa. Wani irin tari Iffah ta farayi mai tahowa da aman jini ta baka ta hancinta harda ta kunne. Jasrah ta fara ƙwala kiran sunan Malikat Bushirat a matuƙar firgice tana sake manne jikinta da bango hanunta na laluben ƙofa amma ta kasa buɗeta... Malikat Bushirat da dama ba barci take ba saboda tsabar damuwa ta buɗe idanunta a hankali jin sautin muryar Jasrah tamkar a sararin samaniya tana yawo. Cigaba da jin sautin ya sata miƙewa zaune ta sauka a gadon baki ɗaya. Babu wani hadimi dake da damar shigowa sashen ɗakunan barcinta sai masu gyarawa kawai suma da safe ne, hakan ya sata ɗora abaya kawai a saman kayan barcinta ta fito.... Jasrah da ta gama fita hayyacinta gaba ɗaya ta faɗa jikin Malikat Bushirat, rungume ƴar uwar tata tayi, a hankali ta shiga hura mata iska a kunne tana bubbuga bayanta. Jasrah da ƴar nutsuwa ta fara zuwa mata tai lamo tana sauke numfarfashi a jajjere, sai kuma ta ɗago a hankali hawaye wanke da fuskarta... “Mike faruwa?”. Malikat ta faɗa a hankali. Ɗakin Jasrah tabi da kallo, kafin ta fara mata bayanin komai har yanzu hawayenta sun kasa tsayawa. Sosai hankalin Malikat ya ƙara tashi, sai dai kamewarta yasa ba lallai ka fahimta a kan fuskarta ba. Cikin takunta na ƙasaita ta isa gaban gadon inda Iffah take. Kwance take samɓal tamkar ba itace ta gama buge-buge ba yanzun. Idanu ta tsura mata a karan farko, yarinya ce ƙarama sosai kuma ƙyaƙyƙyawa matuƙa, duk da halin ciwo da take ciki da canjawar fatar jikinta ƙyawunta da kwarjininta basu gushe ba, tausayinta mai tsanani da ƙaunarta suka sake ratsa zuciyarta. Zaune ta kai gefen gadon ta kai hannu ta shafa yalwataccen gashin Iffah daya gama bajewa a kan filon. “Ibnati kiyi haƙuri zaki samu lafiya bazasu taɓa samun galaba ba kinji”. Iffah da sarai take jin maganar Malikat dan ba barci take ba azaba ce kawai ke ratsata tai murmushin ƙarfin hali a zuciyarta, a karan farko taji ƙaunar matar a ranta da sake ganin kima da girmanta....... ★★_______★★ “Sun jiƙa mana aiki! Sun ɓata mana shiri! Ya ƙwace mana damarmu wadda sake samun samuwarta a garemu cikin sauƙi haka zata iya zame mana mai wahala!!”. Kakkausar muryar Uwa mai matuƙar rashin daɗin saurare ta fara karaɗe ɗakin cikin amon sauti mai tashi sama. A firgice ta miƙe a zabure tare da zube gwuyawunta ƙasa jikinta na tsuma dan dama zaune take ido biyu tana jiran tsammani. “A gafarce ni uwa ba laifina bane, ni kaina ina cikin damuwar tangarɗar da aka samu”. “Bana buƙatar jin komai daga gareki Taƙurya. Domin sakacinki ne ya jawo hakan. Nasha faɗa miki ki san suwa zaki bama aikin da ke bazaki iya yinsa kai tsaye ba. Su kuma waɗan can sakarkarun barinsu sukai wayewar gari tamkar rasa sauran damar data rage miki ne....” Ɗan zabura tayi da nufin cewa wani abu, sai dai tamkar walƙiya Uwa ta ɓace a ɗakin. Hakan na nufin ranta a ɓace yake. Itama kanta ta dafe nata ran na suya da ƙara girmamar baƙin cikinta. Miyasa kowa bai bata matsala ba sai wannan ƴar shilar yarinyar da bata wuce sauron gidanta ba da feshi ɗaya take kawar da shi. Zuciyarta ta fara raya mata Uwa kodai tsoron yarinyar nan takeyi, yo inba tsoro ba taya zata dinga wani gewaye-gewaye bayan bai wuce da ƙyaftawar ido kawai ta shafe babin rayuwarta ba. Dama mutum na gagarar aljani ne banda ta fara maidata susu...... WASHE GARI.. Duk wanda ya kwana ya tashi a masarauta a yau ya tashi ne da tashin hankalin da yafi na jiya sakamakon mawuyacin yanayin da Iffah ta wayi gari. Dole tun gabatowar sallar asuba aka maidata cikin clinic ɗin dake a masarautar saboda ɓallewar jini ta kowane sashe na jikinta. Da farko aman jini ta fara, sai kuma ta hancinta, sai gashi ta ido da kunne harda ma ramin cibiyarta. Hankalin Jasrah da Malikat dake tare da ita ya kai matuƙar ƙololuwar tashi. Duk da kowa yasan ciwo ne bana asibiti ba haka likitoci suka rufu a kanta domin ƙoƙarin ganin sun tsaida jinin amma abu na neman gagara. Har kusan goma na safe a gogon ƙasar babu wani cigaba, jikin Iffah ma ya fara saki alamar jininta yayi ƙasa matuƙa.... ★★... “Bari-Hamshira! Inaga ya kamata a bama masu maganin dake waje dama suma suzo su gwada sa'arsu tunda ba'a dace dana cikin masarauta ba.” Malikat da damuwar duniya ta tattaro a kanta yau ko fadarta bata iya fitaba tana cikin ɗakin barcinta har zuwa yanzu ta ɗago idanunta dake jajur ta sauke akan ƙanwarta ta uku mai suna Zaimah, cikin nuna sallamawa ta jinjina kanta. “Wannan ma shawara ce mai ƙyau Akia, ruɗewa tasa sam wannan tunanin bai zomin ba. A sanar da Ghazi su faɗama Baba Yaro. Sai dai komai ya kasance cikin sirri da amana dan kar maƙiyanmu suyi amfani da wannan damar wajen ruguza ɗan sauran ƙwarin gwiwar mu akan wannan yarinya”. Kai Zaimah ta jinjina mata, sai kuma ta miƙe da hanzari domin isar da umarnin..... *_ƘAUYEN JUMNA_* Tafiya saurayin yake tamkar zai tashi sama dan gaggawa, wani lokacin har tuntuɓe yakanci sai dai kafin ya kai ƙasa yay azamar taro kansa ta hanyar dafe duk abinda ke kusa da shi. Wurjanjan ya isa ƙofar gidan Dattijon da kowa yafi sani da suna Abu Huzaifah ya kwaɗa sallama da iya ƙarfin muryarsa har sau huɗu babu ko jiran a amsa masa. Dattijo Abu Huzaifah Da mukafi sani da Kaka ya dakata da ga ɗinkin kwalliyar doki daya duƙufa yi ya dago suka kalla juna da Iyyani dake shara a tsakar gidan. “Kamarfa sallama naji Abu Jamaima a ƙofar gidan nan” Kafaɗa yaɗan rausayar gefe da ajiye zungureriyar allurar da yake ɗinkin da ita. Kafin ya ce wani abu aka ƙara zungura sallamar a jajjere tamkar yaƙi. Kansa ya ƙara jijjigawa ya miƙe dajan tsaki. “Kai wasu dai mutanen sam basu da lissafi, irin wannan ai saka ɗauka tashin hankali ne”. Kaka ya faɗa cikin mita yana gyara takalmansa. Iyyani da takaici ya ƙulle itama ta bisa da kallo harya fice a soron gidan... “Ayyub! dama kai ne kake ƙwaɗa irin wannan sallama haka? Lafiya dai ko?”. “Da sauƙi dai Baba, amma amin afuwa bani da wani zaɓi bayan hakan. Saƙone daga Baba yaro”. Ya ƙare maganar da miƙama Kaka takardar hanunsa. Kaka ya amsa takardar yana ɗan juyata, sai kuma ya nuna hanyar shiga da faɗin, “Kaga shigo daga ciki”. A tare suka shiga cikin gidan, Kaka ya buɗe takarda yana dubawa, yayinda Iyyani ta kawoma baƙo dake gaisheta ruwa. Kaka ya ɗan murmusa bayan gama karanta takarda tare da girgiza kansa. “Ayyub naga saƙo, sai dai kuma inaga basai naje da kaina ba. Zan baka saƙo ka kai masa nima. Ita kuma ALLAH ya bata lafiya yasa ya zama kaffara a gareta”. Ɗan jimm Ayyub yayi, sai dai kafin yace wani abu Kaka ya miƙe. Ɗakinsa ya shiga, kusan mintuna ashirin sai gashi ya fito da wata jakkar fata. “Kayi maza ka kai masa wannan. Kace kuma ina gaishesa”. Cike da girmamawa Ayyub ya amsa da faɗin “Angama Baba. A huta lafiya”. Kai kawai Kaka ya jinjina masa yana murmushi. Sai da ya rakasa har ƙofar gida sannan ya dawo. Iyyani da duk ta shiga damuwa ko zama baiyiba ta jeho masa tambaya, dan tasan ma'anar wannan murmushin nasa bana farin ciki bane, yakan yisane a lokacin da wani abu ke masa ƙuna a zuciya. “Itama sun taɓata ko?”. Bai bata amsa ba sai da ya zauna. Ya jawo allurarsa zai cigaba da ɗinkinsa. “Dama ai bazasu barta haka ba saboda wasu dalilai”. “Dalilai kuma? Nami to?”. “Kinga sarkin tambaya bani zaren cen dana manta kan bunu”. Iyyani tasan tambayarce baya son amsa mata, dan haka taja bakinta tai shiru bayan ta kawo masa zaren. Sai dai sam zuciyarta babu nutsuwa...... ★★.MASARAUTA.★★ Bayan sallar azhar Ayyub ya iso masarauta. Zuwa yanzun har an fara raɗe raɗin mutuwar Iffah, duk da kuwa ya tadda masu maganin da suka isa suka tumbatsa da matuƙar yawa an tarasu kowa nata gwada ƙoƙarinsa da baiwar da ALLAH ya basa. Baba Yayaroya furzar da nannauyan numfashi bayan ya amshi saƙon kaka a hanun Ayyub “Dama nasan da wuya Dattijo ya zo”. “Amma duk da haka ka aika masa Baba?”. “Ya cancanci a aika masan”. “To amma miyasa yaƙi zuwa? Bayan kuma alamu sun nuna kai tsaye ma yasan abinda ke faruwa anan ɗin”. Baba ya tsurama ɗan nasa ido na wasu sakanni, sai kuma ya girgiza kansa. “Ba lallai sani irin wanda kake tunani yayi ba. Dan nidai nasan baida wata alaƙa da abinda ke faruwa anan. Sai dai ya sani ta dalilin baiwar da ALLAH ya masa duk da shi yana gudunta ne”. “Amma Baba....” “Kaga Ayyub wannan ba lokacin tambayoyi bane. Bara naje muga ko za'a dace anan.” Da kallo Ayyub yabi mahaifin nasa. Sai dai ƙasan ransa fal tambayoyine da yasan samun amsarsu zaiyi wuya a lokacin da yake buƙata. Yasan mahaifinsa gawurtaccen masanin magani ne irin na gargajiya dama na gusar da junnu. Shahararsa tasa Daular Ruman ɗaukarsa da bashi matsayin (Mai magani a gonar yaro) amma ya rasa minene dalilinsa na bama wancan dattijon girma mai tsanani duk da shi kowa bai sanshi ba sai da sunan mai ɗinka kayan doki..... *_ZAWJATA-ALMILKI_* Zuwa yanzu numfashin Iffah ma yana fitane da taimakon na'urori, yayinda jinin dake fita a jikinta har yanzu yake fita ta kunenta. Na ido da hanci da baki ne kawai likitoci suka samu nasarar tsaidawa. Baba yaro shine shugaba na masu maganin, dan haka ake basa damar shiga kai maganin da duk aka bayar dan ai mata amma da taimakon Jasrah kai tsaye. Yanzu ɗinma dai hakance ta kasance. Bayan neman iso aka bashi iznin shiga inda Iffah take, sai dai babu mai iya ganinta kasancewar zagaye take da glass..... *_SHAHAN-SHAN_* Bani kaɗai ba, nasan duk masu karatu tambayarsu zata rinjayane akan wai shin duk abin nan dake faruwa ina _Shahan-shan_ yake ne a matsayinsa na shugaba ga ƙasar ruman baki ɗaya bama daular ruman ba?. To amsar itace yana nan a cikin masarautar, sai dai kuma tun a yammacin jiya bayan dawowa daga sallar juma'a babu wanda ya sakejin motsinsa. Duk da dama fitarsa a zahiri ta zuwa massallaci ce kawai. Yana kuma da ƙofar dake kaisa har massallaci daga sashensa batare daya fito wani ya gansa kai tsaye a masarautar ba. Shiyyasa har zuwa yanzu wanda suka san fuskarsa ko'a cikin masarautar ma ƙalilanne musamman a cikin hadimai. Duk abinda ke faruwa a masarautar kuma kowa nada yaƙinin ya sani, sai dai ba'an miyasa ya zaɓi yin shiru ba. Kamar jiya yau ma labari yajema Malikat Bushirat akan Shahan-shan bai fito sallaba har ta asubahi. A yanzu kam hankalinta ya tashi ba kamar a jiya ba data ɗauka dan yana fushi da auren da yaso bijiremawa ne. A take ta bada umarnin shirya mata zama da shi. Dan ita a karan kanta na uwa garesa bata da hurumin ganinsa a duk sanda taso ko kai tsaye bisa doka da al'adar masarauta da ƙarfin iko na Shahan-shan. Sai zuwa ɗaya tak na kowanne wata da yakanyi kawai na zahiri. Amma duk da haka Tajwar Eshaan kan saci jiki wani lokacin ya kawo mata ziyarar tsakkiyar dare cikin ɓadda kama batare da wani ya taɓa fahimtaba har yanzu a cikin masarautar. Shiri ta farayi duk da batada tabbacin samun damar ganin nasa a yanzu, sai dai sanin duk ƴan majalissar fada na'a masarautar yau yasa bata fidda tsammani ba. Cikin sa'a kuwa cikin abinda baifi mintuna ashirin ba Ghazi ya zo ya isar mata da sakon ƙarɓuwar buƙatarta. Dan dama suma ƴan majalisar fadan nada buƙatar samun wanda zai duba shi, hakan kuma bamai yuwuwa bane dan ita dake amsa suna mahaifiyarsa da Malikat Haseena (Kakarsa) da matansa ne kawai ke da wannan hurumin saboda an tabbatar tun jiya baiko zo falo na uku ba. Sannan duk abincin da mai dafa masa ya shirya tun daga kan na daren jiya har safiyar yau da rana haka yake zuwa ya kwashesa ba'a taɓa ba. Cikin shiri na alfarma da rakkiyar tawagar hadimai maza da mata Malikat Bushirat ta doshi sashen Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed.........✍ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_18_* ..........Tuni labari ya kai kunnuwan sauran matan gidan musamman Malikat Ashwaq da Ameera Danish-Ara da Ameera Haifah cewar Malikat Bushirat ta ziyarci Shahan-shan saboda rashin jin motsinsa. Hakama wasu a cikin matan manyan masu faɗa aji a gidan harma da mazan, wasu iyaye, wasu ƴaƴa, wasu jikoki. Hakan yasa aka kafa gungu-gungu na cigaba da tattaunawa tare da sukar cewar yasan tsiyar daya aikata ai shiyyasa ya ɓoye kansa. Kokuma dodon tsafin nasa ne ya bashi wannan umarnin naƙin fitowa har sai yarinyar mutane ta mutu... Wasu kuwa murmushine kawai nasu dan su kaɗai suka san kansu. Yayinda wasu ke tausayama Tajwar Eshaan ɗin da ganin abubuwa ne suka masa zafi da yawa dan suna kallon komai a matsayin makirci da mafi yawa akafi dangantashi da matan ubansa, da kuma ƴan uwan mahaifin nasa na jini masu zawarcin son hawa wannan kujera... (To koma dai miye ALLAHU shine mafi sani). Duk inda ta gitta hadimai zubewa suke akan gwuyawunsu suna miƙa gaisuwa. Ko sau ɗaya bata ɗaga ido ta kalla kowa ba, sai hadimanta ne ke amsawa duk wanda yay gaisuwar. Tun'a harabar shiga sashen dukkanin hadimanta suka dakata. Sashen Shahan-shan shine mafi ƙyawu da ƙawatuwa na ƙyale-ƙyale a daular ruman. Gini ne da kusan zamuce an yisa da zallar gilashi. Yanada hawa huɗu dan haka sai da lifter. Zaman lissafin dukiya da daular da aka zuba a cikinsa da kuma ainahin fadar da Shahan-shan ke zaman fadanci ma ɓata lokacine. A lokuta da dama duk abinda ke faruwa a cikin masarauta Tajwar na kallo daga cikin sashensa musamman idan a hawa na ƙarshe yake, hatta da wajen masarauta yana iya hangowa. Hadiman dake tsaron sashen matsayin sojoji suka maye gurbinsu wajen take mata baya har falon farko. Anan ɗin ma hadiman zubewa suka dingayi ƙasa kawunansu a risine domin girmamawa a gareta har zuwa falon farko. Wanda suka rakota ciki suka dakata, na falon farkon dake a hawa na ɗaya suka take mata baya har zuwa falo na biyu a hawa na biyu, suma iyakarsu nan, wanda suke a falo na biyu sukai mata rakkiya har zuwa falo na uku dake a hawa na uku. Anan soja ɗaya ne, shine amintacce da yake iya haurawa har zuwa falo na huɗu hawa na huɗu a falon dake can. Anan ma akwai hadimi ƙwara ɗaya sai masu dafa masa abinci su biyu suma. Sune amintattun na ƙarshe dake iya zuwa hawa na can ƙarshe na huɗu kenan, suke iya ganin Tajwar kai tsaye kuma, suke iya sanin a wane ɗaki ya kwana, suke iya shiga ɗakin barcinsa suyi gyara ko kai abinda yake buƙata, ko isar da wani saƙo. Bayan gaisuwa a gareta Ghazi ya nema afuwa da bashi damar zuwa nema mata iso ga Tajwar. Hannu kawai ta iya ɗaga masa. Mintuna da basu wuce huɗu da shigar tasa ba ya dawo ya zube a gabanta. “ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai amfani, shugaba ya bada damar shiga dake har ciki”. Shiru tai kamar bazata motsa ba, dan a duk sanda ta kama zasu gana anan sashensa yakan fito ne su haɗu a wannan falon ko ƙaramin falon hutawarsa dake a hawa na uku. Wannan kuwa a ƙa'ida ko matarsa bata shigarsa, dan haka jin wannan amasa yasata fahimtar akwai matsalar da gaske. Bayan buɗe mata ƙofa Ghazi yaja da baya. Cikin takunta na ƙasaita da isa ta ƙarasa shiga cikin matsakaicin falon mai fidda wani irin ƙamshi da wadataccen sanyin na'urar ac. Rashin girman falon ba komai bane, haɗuwarsa da tsaruwarsa ce mafi ɗaukar hankalin mai kallo. Dan an ƙawatashine da wasu irin tausasan tumtum na ainahin sarakan asali, dardumar falon kanta abin kallo ce, komai ya tsaru dai-dai da tsaruwar manyan mutane. A hankali takai zaune tana mai sauke ajiyar zuciya, sosai takejin matuƙar kewar gudan jinin nata, sai dai tsarin masarautar tasu ya tilasta mata haƙura akan dole tamkar kowace uwa ta Tajwar irinta da akai a cikin wannan daula.... Motsin buɗe ƙofa da ƙamshin turarensa mai rige-rigen isowa hancinta da sautin takumsa ya sata ɗago ƙyawawan idanunta ta sauke a kansa. A hankali ya cigaba da takowa cikin ƙasaita da nutsuwa har ya ƙaraso gareta. Daga tsayen da yake ya ɗan risinar da kansa alamar girmamawa. “Amincin ALLAH ya tabbata a gareki *_Ammie!_*”. Nutsatstsiyar muryarsa mai zurfi da rashin hayaniya ta fita a fisge, dan yanda ya motsa lips ɗinsa a hankali zama ka iya ɗauka bashi yay maganar ba. A hankali ta sauke ajiyar zuciya mai haɗe da nannauyan numfashi ta jinjina kanta da lumshe idanunta ta buɗe a kansa alamar amsawa. A nutse ya kai zaune a gefenta, yay zama irin na ƙasaita da kame kai da kuma girmamawa a gareta matsayin mahaifiya. Hanunta ta ɗaura bisa tattausar sumar dake kansa kwance, tare da ɗan ranƙwafawa ta sumbaci goshinsa da yay zafi zau alamar baida lafiya. Lumsassun idanunsa da ƙanƙancewarsu ya hanata ganin hasken cikinsu ya buɗe, ya motsa lips ɗinsa kaɗan alamar murmushi a gareta. Murmushin ta saki itama a karo na farko da gyara zamanta na ƙasaita. “Kaima amincin ALLAH ya tabbata a gareka *Bugun zuciyar Ammie'n sa*”. Ɗan luuu yay da idanunsa ya lumshesu tare da sake buɗewa a kanta da ɗan risinar da kai na girmamawa. Sai kuma ya kamo hanunta data janye a saman sumar kansa ya sumbata. Ajiyar zuciya ta sake saukewa mai kauri da jin ƙarin ƙaunar tilon gudan jinin nata da maƙiya suka sako a gaba. Tana matuƙar ƙishirwar rashin ganinsa a kusa da ita ko yaushe, sai dai babu yanda ta'iyane..... “Ammie kina lafiya?”. Ya katse mata tunanin da take neman yin nisa a ciki. Numfashi ta ɗan fisga ta fesar alamar dawowa. Sai kuma ta girgiza kanta da raunana fuskarta. “Kasancewarka lafiya itace tawa Saiful-mulk”. A karo na biyu ya saki murmushi yana ɗan jinjina kansa shima, sai kuma ya ɗago ya ɗan kalleta ya kauda kai. “Ina lafiya Ammie”. “Ni ba haka na gani a cikin idanunka ba *_Negar_*”. Baice komaiba kusan minti ɗaya, hakan ya fahintar da ita bazai ce ɗin ba, tai murmushi kawai tana kaɗa kanta. Ta yarda jinin mulki gaskiya ne, dan tana ganinsa yana yawo a cikin gudan jininta. Duk ƙasaita da miskilanci irin na Tajwar Haysam da ita kanta da ake faɗi Eshaan ɗinta ya takasu ya shanye. Irin miskalayen mutanen nan ne shi masu matukar ban mamaki da wuyar sha'ani, dan kai tsaye baka isa gane ainahinsu ba balle farin cikinsu ko damuwarsu kai tsaye, a matsayinta na mahaifiya a garesa da ake ganin yafi sakewa da ita fiye da kowa sukanyi zaman awa guda bai firta jimlar magana sau goma ba, murmushi kam ita da Malikat Haseenah kawai ke gani daga garesa sai mahaifinsa kafin yabar duniya...... Lurar da yay tayi nisa a tunani ya sashi kai hannunsa cikin ƙyaƙyƙyawan bowl ɗin da aka cuɗa dabino da zuba ya ɗakko tsagin dabino ɗaya daya naɗi zuma yay luntsum, ya tare da ɗayan hanunsa ya kai bakinta. A hankali taja numfashi ta sauke alamar dawowa. Babu musu ta matso tare da buɗe bakin ya saka mata. Sai da ta cinye a nutse tana mai kallonsa da murmushi sannan itama ta ɗauka kamar yanda ya bata ta bashi har sau uku. Tasan yunwa yake ji, amma yaƙi cin komai saboda damuwa. Tun yana yaro haka yake, a duk sanda sukaje dubashi a inda ya girma ita da Tajwar Haysam ta wannan hanyar take gane yanada damuwa, ko kuma yana fushi. Dan in har yana jin yunwa yaƙi cin abinci suka matsa masa akan yaci zai ɗiba abincin ya saka a bakinsu, sukuma hakan da yayi zai nusashesu zama su bashi da kansu har sai ya ƙoshi. Tissue tasa ta goge masa bakinsa idonta dake kansa na cika da ƙwalla. “Kanajin yuwa Negar?”. Gajeren murmushisa ya sakar mata da kauda kansa gefe maimakon amsar data buƙaci ji daga garesa. Itama bata sake cewa komaiba, sai wayar landline dake gefensa ta ɗauka. (Inba akan Tajwar Eshaan ba waya isa ganin Malikat Bushirat a haka😑). Cikin ƙanƙanin lokaci aka iso da abinda ta buƙata. Shi dai kallonta yake a harɗe kamar yanda itama take zaune a harɗen. Abincine na musamman, wanda tasan shine mafi soyuwa a garesa... “Idan kana zama da yunwa bazan yafema kaina ba”. Idanunsa yay kamar zai rufe sai kuma ya buɗe a kanta. Ƙasaita jininsa ce, kamewa da tsumewa nagartarsa ce. Kwarjini da cikar haiba mutuncinsa ne. Miskilanci gadonsa ne. inba ita ɗin bama wake ganin murmushin kojin furucin bakinsa, dan babu abu mafi wahala da girma ga Tajwar Eshaan kamar magana. Dariya kam ko'ita a karan kanta zata iya rantsuwa bata taɓa gani ba tunda ba'a gabanta ya tashi ba, sai lokaci-lokaci suke zuwa su gansa. Abincin ta haɗa masa a gabansa da kanta, babu musu kuwa ya amsa tausasan idanunsa na kallonta da jin ƙaunarta kamar kowane ɗa akan mahaifiyarsa. Tsahon mintuna yana tsakurar abincin cike da ƙasaita kamar wani magani, kafin ya ɗauka tissue ya goge bakinsa da janye jikinsa da ga kwanikan alamar ya ƙoshi..... “Ya take yanzun?”. Tambayar da take son jin tun ɗazu daga bakinsa ta fito tamkar an fisgota. Idanunta ta ɗan kafe kansa, amma sai ya kauda kai gefe kamar bashi ya buƙaci ji ba. Taja numfashi ta fesar, itama batare data sake cewa komai ba ta cigaba da nazartar sa. Kusan mintuna uku tsakani sannan ta nisa... “Ban san mikafi buƙatar ji ba. Sauƙin ko akasin sa. Amma dai zan iya cewa muna jiran ikon UBANGIJI ne”. Shiru babu alamar zai sake cewa komai, itama bata sake cewar ba. Kansa ya ɗan risinar gefe bayan ɗan kallon gefen idanu da yay mata. Miƙewa Malikat Bushirat tayi, ya bita da kallo harta isa bakin ƙofa sai kuma ta juyo, “Ina jin tsoron ace alaƙar da maƙiyanmu ke alaƙantawa da kai ta zam haka take Saiful-mulk” Kansa ya ɗauke gefe, itama sai ta ɗauke nata kan daga garesa tana danne lips ɗinta da haƙori. Shiru kusan na minti ɗaya, ita bata fitaba ita bata juyo ba, shi kuma bai amsa mata ba bai kuma motsa ba, sai kawai ta buɗe ƙofar zata fice. “A huta lafiya”. Ya faɗa dai-dai tana ficewa. Bayan kusan minti uku da fitarta ya furzar da nannauyar iska, miƙewa yay hannayensa goye da bayansa ya fara tattaki zuwa gaban window ta saitin inda zai iya hangota. Dai-dai kuwa hadimanta dake zaman jiranta na zagayeta. Duk da nisan da sukema idanunsa bai bar wajen ba har sai da yaga ta shige sashenta da tawagar hadimanta.. Wani irin ƙasaitaccen murmushi ya saki da lumshe idanu, sai kuma ya buɗe cike da isa yana mai barin windown ya shige ƙofar daya fito ɗazun.... Lafiyayyen bedroom ne mai ɗauke da kayan more rayuwa irin nasu na manya. Ƙamshi dai kam ba'a magana dan Tajwar Eshaan ko gonar turare haka ta gansa ta bari saboda yanda yake wanka da shi a duk motsinsa, son ƙamshi da zama cikinsa tamkar al'adarsu ce data zama dole ga talaka da mai kuɗi, sai dai banbancin tsada da ƙamshi ya banbanta maka wanene tare da kai. Amma dai-dai da banɗakin jinin Ruman ko shagon sai da kaya a kasuwa ka shiga saika san kazo ƙasar ƙamshi, duniya ta sansu da wannan tun shekaru aru-aru, dan suna a sahun farko na ƙasashen dake yin turare, yana kuma ɗaya daga cikin tattalin arziƙinsu dake shigar musu da kuɗi da bayyanasu a ko'ina suka shiga a duniya. Zaune ya kai a kujerar dake ɗan gefe ta jikin window, ya kai bayansa kwance a kujerar, tare da kwantar da kansa ya kalli sama ya lumshe idanunsa. Daga ƙasa ƙafafunsa a harɗe, hannayensa duk biyu akan hanun kujerar ya ɗan fara lila kansa. Sai da ya ɗauki tsahon mintuna ashirin a haka dan zakama iya ɗauka barci yake yi kafin ya buɗe idanunsa da suka kaɗa sukai jajur, zaune ya tashi da ƙyau, ya kai hannu drawer'n dake gefen kujerar ya buɗe, ƙaramar waya ƙirar nokia ya ɗakko. Danne-danne yay tare da kaiwa kunnensa yana wani yamutsa fuska. Bugu ɗaya kuwa aka ɗaga daga can, cikin bada umarni da ƙarfin ikon ya furta.. “A kawar da ukun bana buƙatarsu. Haɗuwa, da lokaci zaizo a saƙo”. Ya janye wayar daga kunnensa da dafe kansa yana cizar lips ɗinsa a lokaci guda fuskarsa babu alamar ɗigon wasa ko sassauci a cikinta sai razani mai ban tsoro da saka firgicin ga duk wanda zai iya ganinsa a hakan...........✍ (Tofa! Tajwar......🤔 bara dai nai shiru🤫). *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_19_* ..........Shigar Malikat Bushirat sashen Tajwar da yanayin data fito ya sake zama wasu ƙananun maganganu a masarautar, musamman ga masu ikon faɗa aji. Dan ta ko'ina suna da masu leƙen asiri a cikin hadimai da masu tsaron gidan kamar yanda itama Malikat ɗin ke dasu a kowanne sashe. Ga hadimai dai babu damar yin faɗa da kuwwa sai ƴar ƙus-ƙus, ƙus-ƙus ɗin ma sai ka samu wanda kafi yarda da shi kuɗan zanta gudun karka faɗa tarko. ★★...... Tun barowarta sashen Tajwar ta kasa zaune ta kasa tsaye. Abubuwane birjik ke faman mata kaikawo a zuciya. A karo na farko kenan da zuciyarta ta fara rawa akan al'amarin dake faruwa tun daga randa aka ɗora tilon ɗanta karagar mulkin kujerar Shahan-shan. Anya kuwa ba'akwai lauje cikin naɗi ba a wannan al'amarin?. Sannan ba zaton wuta a maƙera sukema komai ba alhalin yana a masaƙa?. Ta rumtse idanunta da sukai matuƙar ja da ƙarfi, saboda zuciyarta ke hasaso abun, amma ƙirjinta ne keci da wutar ƙunar dangantashi da abinda tafi so fiye da komai a duniya. Sai dai ya zatai, hakan kamar dole ne a gareta kodan rashin samun wani bakin zare har yanzu.... Kalmar bakin zare data faɗo a tunaninta ce ta sata buɗe idanu da sauri, sai kuma ta jawo ɗaya daga cikin wayoyinta da dan tsumar jiki tana gyara zama. Danne-danne tai tare da kaiwa kunnemta. Daga can akai sallama tun kafin ita tayi. A taƙaice ta amsa da faɗin, “Jasrah ina buƙatar hadiman nan yanzun nan”. “An gama Akia”. Jasrah ta amsa mata da girmamawa. Mikewa tai itama ta hau shirin fita fadarta. Sai dai komai tana yinsa ne a tsanake amma yanayinta tattare da matsananciyar damuwa. Fitowarta dai-dai da shigowar Ghazi, ya zube ƙasa yana mai miƙa gaisuwa a gareta. Hannu kawai ta daga masa bayan ta kai zaune. Jasrah ma dake zaman jiran fitowar tata tai mata sannu da fitowa. Kai ta jinjina mata da maida hankalinta ga Ghazi dake gurfane kansa a risine. Itama Jasrah hankalinta ta maida kansa. “Ghazi ya naganka kai ɗaya?”. “Ranki ya daɗe an samu matsala ne”. “Matsala kuma? Kamar ya kenan?”. Ɗan jimm yay na jimamin faɗar abinda ke bakinsa. Sanin Malikat Bushirat bata buƙatar kawane-kwane a magana ya sashi girgiza kansa idanunsa na canja kala zuwa ja sosai. “Ranki ya daɗe gawar uku daga cikinsu kawai muka samu, tare da hadiman dake tsaron inda aka killace sun su duka biyun. Diwa da ta rage ma bana zaton zata kai labari, kuma da alama yanzu-yanzu aka aikata ta hanyar madarar da aka basu matsayin abincin rana. Ba ƙaramar zabura Jasrah tai ba, yayinda Malikat ta rumtse idanu da sauri ƙirjinta yay wata irin harbawa da ƙarfi tamkar zai buɗe dan firgici. Amma a zahiri miskilancinta da ƙasaitar mulki bazai taɓa haska maka komai ba daga yanayin nata..... ★Kamar yanda labarin mutuwar hadiman nan ya isa kunnen Malikat Bushirat haka ya karaɗe kunen kowa a masarautar. Yayinda likitoci suka rufu akan Diwa da itama gab take da rasa tata rayuwar. Wasu kuma sun duƙufa ne akan binciken madarar da suka sha ta ƙarshe duk da kowa ya san daga cikinta ne akama zuba musu ko minene....... *_ZAWJATA-ALMILKI_* Yayinda ake tsaka da jimamin rasa hadiman da sukai sanadin shigar Iffah a mawuyacin halin da take ciki, ita kuma waraka ALLAH ya saukar a gareta bayan duƙufar Baba yaro akanta da maganin da aka amso a wajen Kaka. Tun a mata hayaƙin farko jinin dake fita a jikinta ya tsaya. Hakan ya basu hope ɗin cigaba da bin dokokin da kaka ya kafa na maganin daki-daki har ALLAH yasa aka dace ta kawo wani nannauyan numfashi da ambaton sunan ALLAH. “Ruwa!”. Shine abinda ta ambata na biyu. Cikin sauri Daneen Ammarah ƙanwa ta biyu ga marigayi Tajwar Haysam da ayanzu ke tare da ita ta zabura da kanta ta ɗauka ɗaya daga cikin bottle water dake a ɗakin ta ɓalle murfin ta kafa mata a baki. Cikin mawuyacin hali Iffah take zuƙar ruwar, sai dai kasancewar shine abinda tafi buƙata a ƙanƙanin lokaci ta shanye sa tas. Yumma da itama dai uwa ce gasu Daneen Ammarah ɗin, sannan matsayin Kaka ga Tajwar Eshaan dan ƙanwace ga Malikat Haseena ta sake ɓalle wani ta zuba a hanunta ta shafa a goshin Iffah dake jiƙe sharkaf da gumi. Ajiyar zuciya ta sake ja a hankali tare da buɗe idanunta da sukai mata matuƙar nauyi. Kaɗan ta buɗe ta maida ta rufe. Alhmdllh suka shiga ambata da mata sannu, yayinda Daneen Ammarah cike da zumuɗi tai kiran Malikat Bushirat. Ita ta fara sanar mawa kafin mahaifiyarsu Malikat Haseena duk da tana cikin halin ciwon ƙafa da bata iya ko miƙewa sai da taimakon wheelchair dama ga tsufa..... Cikin abinda baifi mintuna goma ba ɗakin da Iffah ke kwance ya cika da wasu a manyan masarauta. A fuska dai suna nuna farin cikin farkawar tata ne, amma a ƙasan zuciya mafi yawansu kowa da irin tasa manufar. Malikat Bushirat kuwa harda hawayen farin cikinta, farkawar yarinyar da a kallon farko ta gama shiga ranta ya goge mata sauran damuwar abinda ya faru game da kashe Hadiman da aka aika suka aikata sherin daya jawo komai. A take Malikat Bushirat ta bada ƙyauta mai tsoka ga Baba yaro. Hakama wasu a cikin manyan sun masa ƙyautar. Daneen Ammara ce ta biyu, itama kuma ta bada mai tsoka daya bama kowa mamaki. Ana ƙoƙari daukar Iffah zuwa sashen Malikat Bushirat kamar yanda ta buƙata sai ga saƙo da ga Malikat Haseena cewar akai Zawjata-almilki sashenta. Take fuskokin mutane da yawa ya canja a wajen, saɓanin ta Malikat Bushirat data nuna tsantsar farin ciki da jin ƙaunar surukar tata. Dan dama zuciyarta cike take da fargabar sake kasancewar Iffah babu tsaro. Duk da sashenta ma bazai iya zama kanwar lasa ba ga wani mahaluki a zahiri, sai dai yaƙin sunƙuru. To amma idan ta danganta da abinda zuciyarta ke rawa a kai komawar Iffah sashenta kamar an gudu ba'a tsira bane. Sashen Malikat Haseena kuwa sunyi imanin ko ifiritu da kansa zaiji tsoron gittawa kai tsaye balle wani shiryayye dake a masarautar.... Rashin ƙarfin jiki da rashin dai-daiton tunani yasa Iffah ba fahimtar komai take ba, hasalima tun yunƙurin farko bata sake gwada buɗe idanunta ba suna a lumshe. Sai dai tana jin komai dake gudana har ɗaukarta da akai akan keken asibitin zuwa waje. A mota a ka sakata Daneen Ammarah tare da ita. Sai Malikat Bushirat da tabi bayansu a tata motar da ake tuƙata. Ganin haka sauran ƴan son ganin ƙwaf suma duk suka bisu can dan babu mai fatar yin laifi ga Malikat Haseena....... *_GIDAN BABIY_* Tun bayan barin Iffah gidan ɗan sauran kakkaɓin farin ciki da ƙwarin gwiwar da su Fareeha suka barsu da shi ya ida kakkaɓewa. Ummu bata da aiki sai kuka. A kwana uku kawai duk ta rame saboda ko abinci bata ci yanda ya kamata. Hanash kam ba'a magana dan makamancin irin ciwon Iffah na damuwa ne ke neman bugarsa (Depression). Shi kansa Babiy dake dauriya duk ya zuƙe a tsaye wani lokaci har yi yake kamar zai faɗi. Komai ya tsaya musu cak, kunnuwansu ne kawai a buɗe na jiran kiran jana'izar tilon ƴarsu mace data rage. Dan gushewar kwana uku bai sa sun saka ran ta tsallake ba. Suna tsaka da wannan zaman jigum-jigum akai sallama da Babiy ƙofar gida. Kamar bazai fita ba sai kuma ya miƙe cikin ƙarfin hali ya zura takalma ya fita. Ɗan turus yayi idanunsa kafe akan wanda yay sallamar da shi... Abu Moosa da shima ke kallonsa ya iso gabansa da ƙyar yana tangaɗi. Riƙesa Babiy yay da sauri da faɗin, “Subahanallahi Abu Moosa!”. Bai iya ya amsa masa ba saboda halin da yake ciki. Riƙesa da ƙyau Babiy yay suka shiga ciki yana jera masa sannu. Zai zaunar da shi a soro ya girgiza masa kai cike da ƙarfin hali. “Kamin alfarma mu shiga ciki”. Ya faɗa da ƙyar tamkar numfashinsa zai rabu da gangar jikinsa. Cikin sauri Babiy ya cigaba da riƙesa suka shiga cikin gidan, shigowarsu yasa Ummu miƙewa da sauri ta ɗakko tabarma ta shimfiɗa a ƙasan bishiyar dake tsakar gidan... “Ku bani ruwa dan ALLAH”. Abu Moosa Ya sake faɗa da ƙyar yana fisgar numfashi. Ruwan Ummu ta kawo masa, dai-dai da fitowar Hanash daga ɗaki saboda jin maganganu na tashi a gidan nasu. Da ƙyar ya iya maƙwarwa uku saboda numfashinsa fisga yake. Babiy ya ajiye ruwan da sake tallafosa jikinsa. “Abu Moosa mike faruwa ne haka? Daga ina kake?”. Da ƙyar ya iya ɗaga idanunsa dake zubar da hawaye ya kalla Babiy. Sai kuma ya girgiza kan yana jan numfashi da shashsheka. “Abu Hanash ka gafarceni dan ALLAH, nasan wannan yana cikin numfashin bankwana da nakeyi”. “Babu abinda kamun nikam, dan ALLAH kuma ka daina faɗar wannan magana bara mu kaika asibiti”. Riƙo hanun Babiy dake yunƙurin tashi yay yana girgiza masa kai da ƙyar. “Babu buƙatar hakan, domin ban cancanci kwatankwacin wannan adalcin daga gareka ba, kayi haƙuri ka zauna ka saurari abinda zan faɗa maka da yafi kaini asibiti muhimmanci, nasan kuma insha ALLAHU zai maka amfani da kuɓutar da yarinyarka dama sauran yaran da zasu iya biyo baya a makamancin halin data tsinci kanta”. Numfashin dake neman kufce masa yaja da ƙyar kafin ya cigaba da faɗin, “Abu Hanash ka gafarce ni nine nai sanadin shigar ƴaƴanka wannan halin, dan nine nai shunensu ga masarauta”. Da ga Babiy har Ummu da Hanash wani irin zabura sukai mai bugawa da bugun ƙirji. Ya cigaba da faɗin, “Nayi hakane dan son zuciya da shegen son abin duniya. Sai hassadarka data daɗe a zuciyata saboda sana'armu ta kasance iri ɗaya, ada tare ake amsar zumar mu a masarauta amma daga baya aka koma amsar taka kawai saboda gaskiyarka da rashin algus. Maimakon na gyara nima na zama mutumin kirki kamarka sai na kasa hakan, shaiɗan ya dinga tunzurani akan kayi sammu ne shiyyasa. Tun daga wancan lokaci naketa ƙulla hanyoyin ganin bayanka a matsayin ɗaukar fansa, sai dai duk wadda na ƙulla sai ALLAH ya kuɓutar da kai, hakan ya cigaba da ƙaramin tsanarka, dan haka na cigaba da kutsa kaina cikin masarauta dan kawai naga na ɓataka an wulaƙantaka, nan ma banci nasara ba dai. Kwatsam sai aka samu canji gwamnati, ni kuma nai amfani da wannan dama wajen sake cusa kaina cikin tsakkiyar masarauta harna samu nasarar amsuwa, nasan komai game da mutuwar Zawjata-almilki, dan ina gaba-gaba a hadiman da ke aiki ga masu aikatawar”. Yaja numfashinsa da ke fisga da ƙyar. “Lokacin da aka sakamu aikin binciken yara mata guda biyu masu hankali dan a aurama Tajwar naji a raina lokacin nasarata a kanka ya yi, dan haka na bada sunanka da adireshin gidanka. An ɗauka tsahon kwanaki ana bibiyar yaranka da kai kanka kafin azo gareka. Ko bayan mutuwar ta farko ni na ƙara ƙulla aka sake dawowa ta biyu dan burina kawai naga na durƙusar da kai ƙasa. Ka gafarceni Abu Hanash dan nayi nasara, sai dai ramin muguntar dana gina daga ƙarshe ni na afka ciki......” Babiy da hawaye suka gama wanke masa fuska ya share yana duban Abu Moosa “Kenan kai ne ka ƙulla na uku ma?”. “Wlhy a'a bani da alaƙa da wannan, hasalima ban san ƴar wajenka bace sai ranar da aka kawo kuɗin aure”. “Waye ya kashe min ƴaƴa? Kai kuma miya faru da kai?”.......✍ 🤔Ikon ALLAH, wannan duniya ina zaki kaimu, baka damu da kowa ba amma kana barcine da rashin barcin wasu, kana ci ne da rashin cin abincin wasu. Kana numfashi ne da burin ƙaruwar na wasu. Kana farin ciki da gushewar farin cikin wasu. Kana shiga tarkon wahala da dariyar bakunan wasu. Ya ALLAHU ka ɗoramu akan maƙiyammu, ka hanemu yin hassada da zaluntar wani koda ace shi ɗin ya zaluncemu. ALLAH sarki Babiy namu🤦🏻 *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_20_* ........Abu Moosa dake sonyin magana ya dafe ƙirjinsa da numfashi ke kokawar kufcewa, tari ne ya suɓuce masa sai ga jini. Hankalin Babiy da Ummu ya tashi, amma Hanash ko'a jikinsa. Da ƙyar tarin ya lafa, Babiy dake riƙe da shi yace, “Kayi haƙuri muje asibiti, aman jini fa kake yi”. Murmushi yay mai ciwo da kaɗa ma Babiy kansa da ƙyar. “Abu Hanash zuwa asibiti bazai canja komai ba, dan gubar da aka shayar da ni bata da makari a ko'ina sai a wajensu.” “Ya ALLAH! Guba kuma?” “Wannan shine hukuncin daya dace da masu irin halina ai karka damu, kai dai kawai ka saurareni zan gaya maka ta hanyar da zaka kuɓutar da yarinyarka, ina fatan hakan ya zamar min aikin alkairin dazan samu sassauci a kabarina”. Babiy zai yi magana ya dakatar da shi. “Ka saurareni kawa Ab.....” ya kasa ƙarasawa saboda sabon tarin daya sake sarƙesa. Sosai Babiy ya rikice ya shiga ƙwala kiran Hanash duk da yana a kusa da shi. Hanash dake jin tamkar yasa wuƙa ya ƙarasa numfashin wanan shegen tsoho ya amsa da ƙyar. “Kaga kamashi maza muje asibiti”. “K...k...karku wahal da kan.. Ku. ka saurareni kawai”. Abu Moosa ya tari numfashinsu da ƙyar yana dafe ƙircinsa da tari ke yunƙurowa. Babiy ya buɗe baki zai yi magana cikin taresa shima sai kawai sukaga yarab alamar rai yayi halinsa. Salati suka ɗauka a tare, wanda yay dai-dai da shigowar jami'an tsaro dake na ƴan sanda a ƙasar, bayansu wata mata ce ke rusar kuka... “Ranka ya daɗe dama na faɗa muku, na faɗa muku mutumin nan baya ƙaunar mijina, yanzu kun gani da idonku gashi nan ya kashe mini shi, dama kullum yana faɗa min neman rayuwarsa yake yi, ashe dai shine ɗin zai zama ajalinsa.....” ta zube ƙasa tana cigaba da kuka harda kururuwa....... Hankali tashe su Babiy ke kallon wannan mata da jami'an tsaron, ba shigowarce ta tada hankalinsu ba da farko, dan tunaninsu ya basu duk wanda ya bama Abu Moosa guba shine yasa suka biyo sa. Furicin wannan mata da kai tsaye Babiy ya gane matar Abu Moosa ce ya firgitar dasu. Cikin ƙarfin hali Babiy yace, “Yallaɓai taya daga taimako kuma zan zama mai kisa? Abu Moosa abokina ne tun ƙuruciya kowa ya sani, ban kashesa a da da muke tare ba sai yanzu da a ƙalla nama kai shekara biyar kenan ban sakashi a idona ba sai yanzu dana gansa ayam cikin gidana babu zato.....” “......Shiyyasa akaga gawarsa a cikin gidanka yanzu daka samu damar ganin nasa ko?”. Jami'in ya tari numfashin Babiy da sauri yana wani makirin murmushin ƙeta... “Allahumma ajirni fi musibati wa'akhlifni khairin minha” Babiy ya faɗa a zahiri gumi na karyo masa. Duban jami'in yay zaiyi magana matar ta taresa tana cigaba da kukanta mai cike da bori.... “Ƙarya yake wlhy yallaɓai, shekaran jiya jiyan nan sai da yaje har gidanmu ya faffaɗa masa magana mara daɗi da tabbatar masa shine ajalinsa, idan ya ƙaryata ai munada shaidar hakan”. Hanash da zuciyarsa tazo ta tokare maƙoshi a hasale yayo kan matar, wata shegiyar shaƙa yakai mata saiga idanunta tamkar zasu fito waje. “K! baƙar matsiyaciya, dan kawai anga gawar mutum a waje sai ya tabbatar masu wajen suka kashe shi!!”. Idanuta ta rumtse da ƙarfi jikinta na ɓari, ta fara kakarin azaba dan da gaske ta shaƙu. Tuni jami'an tsaron duk sukai kansu da ƙoƙarin ɓanɓare hanun Hanash a wuyanta amma sun kasa. Ummu kuka ta sanya, yayinda Babiy keta kiran sunan Hanash da faɗin ya saketa amma sam babu alamar yana ma jinsa. Da ƙyar aka iya ɓanɓare Hanash, ta zube gefe tana sauke nunfashi da ƙyar hanunta riƙe da wuyanta. Sai da suka bata ruwan da suka fita suka ɗakko a mota da sauri tasha ta samu dai-daiton numfashi. Cike da gadara ogan tawagar ya bama yaransa umarnin kama Babiy da Hanash. Sosai Ummu ke kuka da roƙonsu amma babu wanda ya saurareta, har ƙofar gidansu daya cika da mutane tun isowar jami'an tsaron ta biyosu amma kamarma basu san tanayi ba. Haka aka saka Babiy da Hanash a mota, sai gawar Abu Moosa a Ambulance da sukazo da ita (Alamar akwai dai lauje cikin naɗi kenan. Inba hakaba miye na zuwa da Ambulance ɗin?🤔). Matan anguwar ne suka rufu kan Ummu data yanke jiki ta faɗi bayan wucewar motocin. Amma koda suka zuba mata ruwa bata farfaɗo ba. Hankalinsu ne ya sake tashi, makwafcinsu ya bada umarnin a sakata a motarsa a kaita asibiti. Da taimakon matan aka sakata a mota, matarsa da wata mata dake anguwar itama mijinta ya rasu suka shiga. Sai lokacinne mutane suka samu bakin magana. Wasu na nuna tausayawa ga wannan ahali, wasu na jin farin ciki badan sun taɓa musu komaiba, sai dan kawai dalilin hassada na rashin dalili. A asibiti kam har an amshesu za'a fara dubata sai sukaga Doctor ɗin ya dakata sakamakon kiran wayarsa da akayi. Kansa ya girgiza musu ya nufi barin ɗakin yana sanar musu yanada uziri. Hankali tashe makwafcin nan nasu da ake kira Abu Zainab ya shiga roƙonsa amma bai sauraresu ba. Sun fara neman taikon Nurses suma sai zuƙewa suke saboda gargaɗin da Doctor yay musu. Al'amarin kamar wasa anƙi taɓa Ummu, dole suka ɗauketa suka bar asibitin zuwa wani, sai dai acan ɗin ma har an amshesu aka koresu. Basu gajiyaba suna kuka suka nufi privet ko acan za'a dace tunda aikin kuɗine. Anan sun amsheta, amma sun sara musu maƙudan kuɗaɗe kafin su taɓata, acewarsu dokarsu kenan. Matar nan da mijinta ya rasu ta fashe da kuka tana girgiza kai. “Suma basa son su amshemu ne kawai, shiyyasa suke mana kora da hali. Inba kora da hali ba ai banajin Abu Hanash ya mallaki koda kwatar waɗan nan kuɗaɗen da suka ambata inba dai kaddararsa zai saida ba”. “Hakane Umm Yazeed maganarki nakan gaskiya, kuma tabbas na fara ji a jikina akwai lauje cikin naɗi a wannan lamarin, da alama hanasu amsarmu akeyi”. Abu Zainab ya faɗa ransa a ɓace. Matar Abu Zainab dake share hawayen itama ta ce, “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Wannan wace irin masiface haka? Mi bayin ALLAH nan suka tarema wani da zafi haka?”. “Sanin gaibu sai ALLAH, inaga inada mafita ɗaya, mu ɗauketa mu maidata gida sai a sanar da ƴan uwansu ko? Tunda mudai munyi iya ƙoƙarin mu...” “Da hakan kukai tun farko da baku wahal da kanku ba”. Wata murya ta faɗa a bayansu. Da sauri suka juya su duka, sai dai bayan mutumin kawai suka iya gani. Da gudu Abu Zainab ya bisa, amma kafin yaƙarasa garesan harya shige mota sai ƙura ya bulesa da shi....... (🤔????) *_MASARAUTA_* Babban ɗaki na musamman aka warema Iffah a sashen Malikat Haseena. Tare da amintattun hadimai biyar da zasu dinga mata hidima. Sai Ghazi biyar suma da zasu dinga bata tsaro duk da dama sashen zagaye yake da masu tsaron, amma an ware biyar ɗinne na musamman domin kula da duk wani motsin shiga da fitar mutane da zai shafi Iffah. Hakan ya sake saka Malikat Bushirat a farin ciki matuƙa. Yayinda sabanin haka ya bayyana a fuskokin munafukai, sai dai wasu sunyi jarumtar dannewa baƙin cikin nacin zukatansu tamkar wutar daji. Malikat Haseena data zartar da hukuncin batama nuna tasan sunai ba. Ita kuwa Daneen Ammarah damar nutsuwar nazartarsu ta samu ɗaya bayan ɗaya dalilin wani ɓoyayyen al'amari dake ajiye a zuciyarta tsahon shekaru. Daneen Ammarah ta kasance ɗaya daga cikin ƴaƴan Malikat Haseena da Tajwar Abdul-majeed Ibn Aliy. Su huɗu suka haifa. Tajwar Haysam shine babba, (sarkin daya shuɗe kuma mahaifin sarkin yanzun). Sai Daneen Waheeda tana auren wani babban sarki a yankin larabawa. Sai Daneen Ammarah, itama tayi aure sai dai auren bai jimaba sakamakon wani ɓoyayyen al'amari dake tattare da ita, wannan ne sanadin dawowarta gida take zaune kusan shekara goma sha tara kenan bata kuma sake wani auren ba. Ƴar uwarta da mahaifiyarsu Malikat Haseena da marigayi Tajwar Haysam da mahaifinsu daya bar duniya da tabon damuwar ƙaddarar ɗiyar tasa ne kawai sukasan wannan sirrin, al'amarin ya sameta tun tana ƙarama dan bata wuce shekara 14 ba, shiyyasa ta jima batayi aure ba, bayan ta samu tai auren kuma bata jimaba suka rabu da mijin dan auren baifi wata takwas ba ma. Manyan masarauta sunta ƙananan magana akan hakan da fassara al'amarin na Daneen Ammarah ta siga daban-daban amma su Malikat Haseena sukai biris dasu. Sai auta Miran Nayyar nada shekara bakwai ALLAH yay masa rasuwa. Bazamuce Iffah tayi garau ba kam a wannan yini. Dan har yanzu ko idanunta bata iya ɗagawa ta kalla kowa. Sai dai daidaituwar fitar numfashinta ya saka nutsuwa a zuciyar kowa. Koba komai dai an samu sassauci ai. Daneen Ammarah itace da kanta ta gogema Iffah jiki ta canja mata kaya, itace kuma da kanta tai zaman bata abinci daya kasance mai ruwa-ruwa. Daga haka aka ƙara bata magungunan da duk suka dace da gyara mata kwanciya a lafiyayyen gadon da yaji shimfiɗu na alfarma. Wani irin barcine mai daɗi yay awon gaba da ita, cikin ƙanƙanin lokaci ta fara sauke numfashi. Daneen Ammarah dake kallonta cike da tausayawa da jin wani ɓoyayyen al'amari akan yarinyar ta sauke numfashi ahankali da mata addu'ar samun lafiya da fatan ya zama kaffara a gareta....... ★★.... ★.... ★★..... Duk wani nau'in kiranye ga uwa ta yisa tun lokacin da labarin abinda ya faru da yarinyar can sakamakon saka riga ya risketa, tabbas sune suka bada riga, amma abinda ya faru da yarinyar bashine ya kamata ya faru ba akan rigar, dan shirinsu sam bashi da alaƙa da halin da take a ciki yanzun. Hakan na nufin kenan bayansu akwai wasu masu shiri akan yarinyar kenan?. In dai har hakane kuwa to su ɗin su wanene? Minene tasu manufar kuma?. Wannan amsar take buƙatar ji a wajen Uwa, sai dai har zuwa duhun dare babu alamar zata ziyarce ta. Tun zuciyarta na raya mata ta jira har ta fara jin ita taje gareta mana kawai. Amma tuna zuwa ga Uwa babban al'amari ne mai wahalar yiwuwa gareta yasa ta kasa iya cigaba da tabuka komai har dare ya cigaba da tsalawa masarautar ta ɗauki shiru tamkar babu wani mahaluki mai sauran numfashi. Ta cigaba da kaikawo a cikin wannan shiru, tare da ƙara gwada dabaru kala-kala na kiranye ga Uwa. Dai-dai lokacin da take sarewa, gaɓɓanta ke nuna gajiyawa mummunan sautin dariyar Uwa mara daɗin saurare a kunnuwa ta fara mata kaikawo tamkar tana yawo cikin iska. Ƙasa ta zube akan gwuyawunta tana mai jan nannauyan numfashi dajin sanyi a ranta. Tarwai Uwa ta bayyana a gabanta, akan kujerar baƙin karfenta mai adon gwal sanye cikin jajayen kaya kamar koyaushe. Mummunar fuskarta a matuƙar tsuke take babu alamar itace ta gama dariyar dataita amsa kuwa a mintocin da suka shuɗe..... “Barka da isowa Uwa mai share kukan masu kuka. Uwa ina cikin matuƙar ruɗani, dan aikinmu yasha banban da wanda ya bayyana ga ƴar shilar suda. Kamar yanda na riski yinin jiya a cikin ruɗani, haka na kasance a duhun dare batare da na rintsa ba, na kuma sake wayar gari da ƙishirwar ganinki a yinin yau har zuwa iyanzu da daren ke ƙoƙarin zama dare biyu da faruwar komai?. Shin kuskuren daga garemu ne? Kokuwa kece kika canja aikin ya koma hakan? Ko akwai wasu masu irin shirinmu ne a wannan daula batare da mun san dasu ba? Minene manufarsu su? Wane buri kuma suke da shirin cimmawa?. Uwa ki taimakeni nasan wannan amsoshi in ba hakaba zuciyata na gab da tarwatsewa ne”. “Bazan gaji da tuna miki akwai ƙalubale zagaye da cikar matakin aykinki na biyu ba, kuma wannan ƴar shila na tare da kaddarar ƙalubalenne, sai dai na miki alkawarin tsayuwar daka akan hana faruwar nasarar da zatazo in har bataki bace ba. Tabbas aikin ba namu bane, kuma rigar da aka kai mata ta sanya ba tamu bace itama. Na gano hakane a daren jiya bayan mutuwar waɗan can hadiman da kuma samun lafiyar ƴar shilar.. Hakane ya sani duƙufa bincike tuƙuru domin gano daga ina matsalar take?, wanene ya shirya aikin laɓewa bayan namu? Har yaci nasarar kuɓutar da ita da tarkon makircin sa cikin sauƙi haka?......” “Uwa kin gano kenan?”. Ta-kurya ta tari numfashinta cike da zalamar son jin amsa........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_21_* ________________________ _Innalillahi wa-inna ilaihirraji'un. A madadin ɗaukacin ɗalibai na G.G.A.S.S D/Z. Muna miƙa saƙon ta'aziyyar ga ƴan uwanmu da iyayenmu da yayyenmu na rasa Uwa abin alfaharin duk wani ɗa na gari da mukai *Hajiya Ai'sha Ahmad Tukur* tsohuwar principal ɗinmu. Ya rabbi ka gafarta mata, ka yafe mata kurakuranta. Ka bama iyalanta da mu haƙurin rashinta. Mu data bama tarbiyya a wani bigire na rayuwa, ALLAH yasa muyi koyi da ƙyawawan halayenta managarta. Dan ita ɗin abin alfaharinmu ce da bazamu taɓa iya mantawa ba😭, zamu tunata, zamu cigaba da tunawa da ita, zakuma mu tunatar dana bayanmu kyawawan halayenta da alkairinta. (ALLAH ya gafarta mata.😭🙏🏻)_ ________________________ ...........“Ina kan ƙoƙarin yin hakan yawaitar kiranyanki ya katse ni, amma tabbas wanda ya aikata yana a cikin wannan daula ne, yana kuma da babban shirin daya kamata mu sani tun a yanzu. Ina kuma ji a jikina babban yaƙine da kema ya shafeki, kuma za'a cigaba da amfani da yarinyar ne wajen tabbatar da shi in har tana cikin masarautar nan”. “Shiyyasa tun farko nace a kawar da ita Uwa, dan babu wani amfani da wannan yarinyar zatamin face cigaba da ɗagamin hankali, gashi kuma har tana neman zama tafinta a al'amurana dake gab da kammala bayan gumurzun yaƙin da naci na tsahon shekaru a baya kafin zuwa lokacin tattara ganima”. “Abinda kike ƙoƙarin yi shine mafi girman kuskure da zai rusa dukkan nasarorinki Ta-kurya. Domin yunƙurin kashe wannan ƴar shilar da kike tamkar kashe rayuwarki ne baki ɗaya. Tun farko na faɗa miki kasheta kai tsaye bashine mafitar ba, ba kuma shine ƙarshen daƙile yunƙurinta ba ita a karan kanta. Hasalima a yanzu rayuwarta mukafi buƙata, zamu jefata ne matsayin dutse ɗaya dazai wargaza tsuntsaye biyu. An wargaza mana shirin mu na farko a kanta, dan haka zamu tafi na biyu. Yaƙinki a yanzu shine kiyi duk yanda zaki ta baro wancan sashen daga nan zuwa cikar kwanaki bakwai. Zakiyi yanka na baƙar babbar dabba a daren goma sha uku, zakuma ki dawo da rigar data sanya. Kiyi duk wani ƙoƙarin da zai hana kusancinta da Ajlaan a turaka. Dan maganar kaita turakarsa ta rushe kuma zamu sake sabon salo ne domin kama tsuntsu mai wayo.......” “An gama Uwa mai share kukan masu kuka. Sai dai dawo da rigar nan zai zama abu mai wahala kasancewar tana a hanun Mamma (Malikat Haseena) ne a yanzu haka”. “Wannan umarni ne Ta-ƙurya”. “Zanyi iya ƙoƙarina Uwa. Sai kuma maganar mutuwar Hadiman can, Shahanshan da kansa ya saka kwamitin bincike masu tsauri da basu taɓa ƙetare nasarar cika umarnin da'aka basu ba. Kinga akwai matsala kenan tunda waɗan can sun laɓe ne a jikin aikinmu suka zartar da nasu, sannan suka kashe hadiman tamkar yanda muka shirya kafin mu mu aiwatar da hakan”. Wata irin mahaukaciyar dariya mai amsa kuwwa Uwa ta shiga ƙyalkyalawa, sai da ta ɗauka tsahon lokaci tanayi kafin ta tsagaita ta tsuke fuska tamkar ba itace tayin ba. Har ta ƙurya ta fidda ran samun amsa sai kuma Uwa ta sake ƙyalkyalewa da dariya tana ambaton “Ajlan! Ajlan!! Ajlan!!!” ta ƙara kwashewa da dariya tana mai disashewa a idanun Ta-kurya da zuciyarta ta kasa fassara ma'ana ko dalilin dariyar ta uwa... 🤔Ko miye naku tunanin a wannan gaɓar kuma masu karatu???. ★... ★.★.★ ★... *_GIDAN BABIY_* Sun dawo har yanzu da ɗan sauran mutane maƙwafta da aketa ɗan ƙus-ƙus akan lamarin. Cikin ƙanƙanin lokaci aka baibaye motar, waɗanda suka shige gidaje suka fara fitowa. A yanayin da aka fidda Ummu mafi yawansu sunma ɗauka dai bata da rai, dan kuwa da gaske babu alamar rai tare da itan. Kuka da salatin da mafi yawan mutane suka ɗauka na tunanin ta mutun ne yasa Abu Zainab saurin dakatar da su. “Dan ALLAH kowa ya kwantar da hankalinsa. Umm-Arfa ba mutuwa tai ba”. Badan hankalin su ya kwantaba sukai shiru, sai dai dama kukan na wasu na munafurci ne dai. Matane suka kamata aka shiga da ita, a tabarmar da suka samu tsakar gida suka shimfiɗeta. Cikin sa'a Abu Zainab yaci karo da wayar Babiy dake yashe a ƙasa. Da alama sanda jami'an nan zasu fita da shine ta faɗi. Jikinsa har tsuma yake a duba contact ɗin wayar, cikin sa'a ya samo number da akai saving da Baba. Baya raba ɗayan biyu mai sunan nada babban matsayin baban a wajen Babiy ɗin, dan haka ya danna masa kira kai tsaye, sai dai harta tsinke ba'a ɗaga ba. Sake kiran yay yana addu'ar dacewa sai ko gashi an ɗaga... ★A lokacin da kiran Abu Zainab ya riski su kaka ta hanyar wayar Babiy ba'a ƙaramin tashin hankali suka tsinci kansu ba shi da Iyyani. Duk da kasancewar yamma tayi kuma yasan a yau dole ne sai ya dangana da daular ruman dole ya bazama neman wani yaro mai mota a ƙauyen nasu dake jigila a ko yaushe, cikin sa'a ya samesa ya dawo kenan ma ko gida bai shiga ba. Amma saboda mutuncinsa da ake gani yana masa bayani babu musu ya amsa masa suka ɗauka hanya harda Iyyani daketa faman sharar hawayen da suka kasa tsaya mata. Ana sallar isha'i suka iso cikin daular ruman. Basu sami mutane ba a gidan kamar ɗazun, sai Umm Yazeed da matar Abu Zainab dake dai tare da ita har yanzun. Zuwa yanzu Ummu ta farfaɗo, sai dai taƙi magana da kowa sai hawaye da taketa faman zirarwa ta gefen ido, ga numfashinta baya fita normal kamar na kowa, tana fitar da shine da fisgosa a wahale sannan a fiffisge. Kuka Iyyani ta sake fashe da shi da rungume Ummu a jikinta tana kiran sunanta. Kaka kam tsaye yay kawai zuciyarsa na harbawa da ƙuna. Suna a haka Abu Zainab ya dawo, dama sallar isha'i yaje. Cikin girmamawa ya gaida kaka, shima ya amsa masa da kulawa da godiya. Ya ɗan murmusa kansa a risine. “Ai ba komai baba yiwa kai ne. Sannan mun zama ɗaya ai mu da Abu Hanash. Ko mu irin haka ta faru da mu zai tsaya tsayin dakane a kan komai. Ruɗanin halin da Umm Arfa ke ciki yasa su bamu bibiyesu musan miya faru ba har yanzu gaskiya. Dan munata yawo a asibitoci amma sunƙi amsarta, ga jikin nata kuma yana buƙatar a duba mata shi, shiyyasa yanzu dana idar da sallar magrib naje na samo ɗan uwana dake aikin asibiti gashi muna tare, sai dai ba wani babban likita bane dai....” Kai kawai Kaka ya jinjina masa da faɗin, “ALLAH ya saka muku da alkairi, haka ake fatan zaman makwaftaka, domin ita makwaftaka tanada ƙarfin da zata iya fin ƴan uwantaka muhimmanci ma a wani ɓangaren. Yanzu gashi abu ya samesu, kafin mu muzo kun basu ɗauki, da bakwa zaman lafiya kuma hakan bazai yuwuba. Dan haka duk wani mutum na ƙwarai daya san kansa ya dace ya rayu da maƙwafcinsa lafiya da ƙaunar juna”. “Hakane Baba, ALLAH ya saka da alkairi. Bara na shigo da shi”. Murmushi Kaka yayi da jinjina masa kai. Koda suka shigo tare da ɗan uwan nasa shima ya gaida Kaka da girmamawa, hakama Iyyani da har yanzu ke faman sharar hawaye tana tofama Ummu addu'a. Damar duba Ummun Kaka ya bashi dan haka ya shiga aikinsa. Ya tabbatar musu jinin Ummu ya hau matuƙa, amma zai mata allurar barci ta samu nutsuwa dan barinta a ido biyu akwai haɗari komai zai iya faruwa. Sai da suka maida Ummu ɗaki sannan ya saka mata ruwa da allurai aciki, cikin sa'a kuwa babu jimawa barci yay awan gaba da ita. Sosai Kaka yay musu godiya da sanya albarka, dan ko sisi ɗan uwan nasa bai amsaba ma....... ★★.... ★.... ★★..... An wayi gari da samun canji sosai a yanayin Iffah, dan zuwa yau kam Alhmdllh. Sai dai jikinta dake wani irin saɓa saikace wata macijiya. Sai kuma rauni data tsinci kanta a ciki sakamakon mummunan mafarkin datai akan su Babiy daya haddasa mata matsanancin faɗuwar gaba da akai-akai. Gata dai iya gata tana gani wajen tsohuwa Malikat Haseena duk da bata da lafiyar ƙafa sai a wheelchair take komai. Hakama Daneen Ammarah tsaye take kan Iffah, yanda take kula da ita yasa Iffah jin ƙaunarta batare data san dalili ba, ganinta take tamkar Ummu. Yanda ake tsaye kanta da gata da kulawa yasa ko damar yin ƙwaƙwaran tunani bata da shi, dan da tayi shiru Daneen Ammarah zata nuna damuwa taita jera mata tambayar mike damunta? Ko tamanin wani abu ne a jikinta har yanzu?. Dole take sassauta damuwarta, sai dai tayi matuƙar dagewa wajen ambaton UBANGIJI kamar yanda Babiy da Ummu suka dinga jaddada mata a nasiharsu ta ƙarshe gareta. Labarin mutuwar hadiman da suka kai mata rigar nan ta saka yazo kunenta itama, sai dai jin sanadin mutuwar tasu ya tsaya mata a rai matuƙa, harma ta rasa yaya zata fassara al'amarin... Bayan idar da sallar isha'i tana zaune tayi tagumi gaba ɗaya hankalinta ya tattara ga tunanin iyayenta da mummunan mafarkin daren jiya a kansu Daneen Ammarah ta shigo hadimai uku biye da ita. A bakin gadon takai zaune tare da kai hannu ta janye tagumin da Iffah tai. Nannauyan nunfashi ta sauke da ɗan ɗagowa ta kalla Daneen Ammarah ɗin, sai kuma ta maida kanta ta risinar da mata sannu da zuwa. Daneen Ammarah dake kallonta cikin damuwa taja numfashi ta fesar batare data amsa ba. Dai-dai nan Hadiman da suke tare suka zube gaban Iffah bayan sun ajiye kayan hanunsu. Gaisheta suke da tsantsar girmamawar da ko iya ɗaga kawunansu basayi su dubi sashen da take. Sam Iffah batajin daɗin yanda suke matan saboda bata sababa, a ranta gani take kamar ƙasƙancine. Hannu Daneen Ammarah ta kaɗa musu alamar suje, zumut suka miƙe tamkar ƙyaftawar ido suka fice. Iffah ta bisu da kallo cike da jin raɗaɗi a zuciyarta. “Ibnati!”. “Na'am Mamy!”. Iffah ta amsa cike da girmamawa ga Daneen Ammarah. Sosai sunan da Iffah ke kiranta da shi ke raunanata da sake jin ƙaunar yarinyar, dan a bakin mutum ɗaya tak take jinsa kafin ita. Taja numfashi da haɗiye hawayen da suka cika mata ido ta maye gurbinsu da murmushi. “Ibnati bana son cigaba da ganin damuwar nan a fuskarki, ki kwantar da hankalinki insha ALLAHU babu abinda zai sake samunki. Wanda ma ya sameki ki ɗauka kaddararkice kinji, amma inaji a jikina insha ALLAH kece mabuɗin nasararmu, ke ce hasken da zata haska mana duhun da muke a ciki a Daular nan kinji”. Kai Iffah ta jinjina a hankali, haka kawai take jin matuƙar nutsuwar kasancewa da wannan baiwar ALLAH, sam batajin irin zafi da tsanar da takema duk wani mai alaƙa da masarauta a kanta. Kallonta take tamkar wata katanga ta wani babban al'amari dake tunkarota. “Mamy bana tare da damuwa in har kina a kusa dani, duk abinda ya sameni kuma dama ALLAH ya ƙaddara sai ya sameni koda banzo nan ba. Ina tunanin su Ummu ne da jin tsananin kewarsu saboda mummunan mafarkin danai akansu jiya, ina tsoron kar wani abu ya samesu ne suma?”. Cike da jin tausayita Daneen Ammarah ta shafa kanta, “Duk ɗa na gari dolene ya kasance cikin kewa a lokacin da yay nesa da ahalinsa, da ace inada dama da a yau sai na kaiki kinga su Ummunki. Amma dokar masarauta ce Zawjata-almilki tana fitane kawai bisa ƙwaƙwaran dalili, zuwa gidansu kuwa tana yinsa ne sau biyu tak a shekara, ɗaya a sirrance, ɗaya a bayyane tare da rakkiyar hadimai. Shiko mafarki ai na gaskiya bane Ibnati, MANZANNI ne kawai idan suka yisa yake gaskiya a garesu, amma mu namu yakanzo da wasu sigogi ciki harda sheɗanu”. A hankali hawaye suka silalo a kumatun Iffah, bawai lokacin ziyarar bane yay mata nisa, rashin tabbacin kaiwa lokacin ziyararne ya sata zubar hawaye. Ita dake zaman jiran ƙaddarar mutuwarta taya zatai tunanin zuwan waɗan can damarmaki guda biyu na ganin su Babiy, maganar mafarki kam ta san gaskiya Mamyn ta faɗa, itama kuma ba tana dangantashi da zama tabbaci bane, kawai tana matuƙar jin tsoron faruwar wani abu ne a dalilin mafarkanta na baya.... Ganin hawayen Iffah ya matuƙar tada hankalin Daneen Ammarah, a rikice ta shiga tambayarta kamar yanda ta saba in har ta ganta a makamancin damuwar nan. Hannu Iffah tasa ta share hawayen nata da ƙirƙiro murmushi. “Mamy ki kwantar da hankalinki hawayen sunzo ne kawai da kansu babu dalili”. “Haba Ibnati, dama ana kuka babu dalili ne? Ko baki faɗaba nasan kinada dalilan yin kuka, amma idan kika zama mai haƙuri da juriya wataran ke zakiyi dariya a gaban waɗanda suka cancanta suyi kuka.” (ALLAH ya tabbatar da wannan ranar) Iffah ta faɗa a zuciyarta, a zahiri kam sai ta goge hawayen tana murmushi. Hakan yasa Daneen Ammarah yin murmushin itama, kafin kuma ta mike tsaye da kama Iffah suka koma kan dardumar da aka shirya abinci acan gefe na ɗakin, dan ɗakine ƙaton gaske mai dauke da komai na jin daɗin duniya. Tare sukaci abincin, Daneen Ammarah har tana bama Iffah wani lokacin a baki, jitake inama Iffah ɗiyartace, dan da'ace tana gidan aurenta har yanzu ɗiyarta ta fari zata iya kasancewa dai-dai da shekarun Iffah ne. Kulawar Daneen Ammarah ta sake saka sassauci a zuciyar Iffah harta ɗan saki jikinta. Bayan sun kammala ta sakata shiga bayi tai wankan maganin da take amfani da shi, data fitoma da kanta tai mata hayaƙin turare. Iffah ta hau gado ta zauna, Daneen Ammarah a gefenta da littafin tarihin annabawa acewarta zata dinga karantama Iffah har sai taga tayi barci domin ɗebe mata kewa. “Yauwa Ibnati kin shirya dai ko?”. Fuskar Iffah da ɗan murmushi tace, “Eh Mamy na” “Masha ALLAHU ashe dai Habibty na tare dani”. Hannu Iffah tasa ta rufe fuska tana murmushi, itama dai Daneen Ammarah murmushin take. Ta fara buɗe littafin. Iffah dake kallonta tai dauriyar finciko ɗaya daga ɗunmbin tabayoyin dake cin ranta ganin zata fara karatun... “Mamy dan ALLAH na tambayeki wani abu?”. “Oh Ibnati tambayeni mana kanki ma tsaye kuwa.” Iffah ta jinjina kanta da sauke ajiyar zuciya..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_22_* .......Iffah ta jinjina kanta da sauke ajiyar zuciya, “Immm Mamy dama...” sai kuma tai shiru dalilin gargaɗin da zuciyarta ke mata tunda har yanzu fa Bama wai tasan matsayin Daneen Ammarah ɗin bane a masarautar. “Dama mi? Kinga karkiji komai kimin duk tambayar da kike buƙata, insha ALLAH zan kasance mai baki amsa, idan kuma bata dace ba zan baki shawara kodan nan gaba”. Kai Iffah ta jinjina “Dama dan ALLAH zance ne yanzu mutuwar su hadiman can shikenan ta tafi a banza baza'ai wani bincike a gano ba?”. Kallo na kusan sakan biyar Daneen Ammarah taima Iffah da har tama ɗauka tai laifi, amma sai taji taja numfashi da maida kanta kan littafin hanunta. “Mutuwarsu bazai tafi a banza ba saboda dalili mai ƙarfi Ibnati. Dan duk wanda ya kashesu yana gudun tonuwar asirinsa ne akan cutar da ke da akai yunkurin yi. A yanzu haka Shahanshan ya saka kwamitin bincike, muna fatan kuma ta wannan hanyar za'a gano koma wanene ya saka ki a halin da kika tsinci kanki. Kuma dama kema ana jiran ƙara samun lafiyarki ne aji ko akwai wani abu da kika sani, ko kuma bayan su ukun can da ɗayar da aka samu nasarar ceto ranta ko akwai wasu..” Da sauri Iffah ta dubeta. “Mamy akwai wadda bata mutu ba dama?”. “Eh akwai amintacciyar hadimar Umm-Jasrah (haka take kiran Malikat Bushirat) mai suna Diwa. Ita an kaita asibiti kafin gubar da suka sha ta karasa katsa ƴan hanjinta. Alhmdllh kuma an dace dan yanzu haka tana kan shan magani, tana kuma zagaye da tsatstsauran tsaro” “ALLAH ya ƙara bata lafiya, sai dai kuma banajin tanada hannu a cikin al'amarin Mamy, dan da ganinta mutiniyar kirki ce”. “Gane mutanen kirki ba'a ido yake ba Ibnati musamman a wannan masarautar da kowa kansa kawai ya sani, a mafi yawan lokuta ma ba'a gane maƙiyi da halayya. Akwai rikitattun abubuwa dake a matuƙar cuɗe a wannan Daular da gani da ido bazai wadaci mai kallo ba, dan haka nakeso ki nutsu kisa hankalinki waje ɗaya kafin ki koma sashenki ki koyi abubuwa da yawa na salon mulki da tsarin matsayinki na Zawjata-almilki. Saboda kunada matuƙar tasiri da girma a tsarin ƙarfin iko na masarauta da kaikawon talakawan ƙasan ruman. Fatana kuma kece Malikat a cikin Zawjata-almilki insha ALLAHU”. Sam Iffah bata fahimci komai ba ga kalaman Daneen Ammarah, amma sai bata sake cewa komai ba dan a ganinta tana buƙatar samun lokacin yin nazari na musamman a kansu kafin ta fahimcesu dallah-dallah....... ★★... ★... ★★.... Ana idar da sallar asuba drivern daya kawo su Kaka jiya dan hanashi komawa yay saboda dare ya ɗauka Iyyani da Ummu suka wuce. Kaka da Abu Zainab kuma sukai shirin fara neman inda zasu samo Babiy da Hanash. Dai-dai suna shiga mota kaka ya dubi Abu Zainab da ɗan murmushin ƙarfin hali a fuskarsa, “To Zakariyya kai ne ɗan gari, yanzu ta ina zamu fara kenan?”. Numfashi Abu Zainab ya furzar, tare da yin ɗan jimm alamar tunani, “E to Baba banace ba dai, dan al'amari nada wuya, saboda bamu da tabbacin waɗan nan jami'ai daga wane station suke. Amma ni yanzu a nawa shawaran ina ganin kamar mu nema gidan shi marigayi ɗin, tunda matarsa ita ta kawo jami'an tasan daga ina suke”. “Hakane, wannan ma shawara ce mai kyau, sai dai inda gizo ke saƙar kai koka san ina gidan Dawood ɗin yake? Dan ni dai rabona da shi ma kusan shekara biyar kenan tun suna tare da Muhammad Zayyan”. “Ito baba banace ba, dan kusan nima hakan dai take, amma bayan tashinsa daga anguwarmu nasan inda ya koma, sai dai bani da tabbacin ko har yanzu acan ɗin yake zaune tunda ba wani huɗɗa muke ba gaskiya, dama dalilin Abu Hanash ɗinne ake gaisawa sai kuma idan wani zama na anguwa ya haɗa kafin ya tashi kenan. Amma yanzu dai bara mu tafi can ɗin kawai rana ma nayi”. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso anguwar, kasancewar ma ta cika ba kamar da ba da kyar suka iya samo gidan. Duk da jikinsu ya ɗanyi sanyi ganin ƙofar gidan babu alamar anyi wani abu daya shafi mutuwa Abu Zainab yay sallama har sau uku. Ana huɗun wani mutum ya fito. Cikin binsu da kallon rashin sani ya basu hannu suka gaisa. Abu Zainab da shima dai jikinsa yay sanyi ya ce, “Kayi haƙuri nasan baka sammu ba. Muma dai munzo nan ɗinne neman wani bawan ALLAH daya zauna anan shekara kusan huɗu haka baya. Sunansa Dawood, amma ana masa alkunya da Abu Moosa. Matarsa ɗaya bashi kuma da yaro ko ɗaya”. “ALLAH sarki, gaskiya ban sanshi ba, dan nima dai ban wuce shekara biyu da tarewa anan ɗin ba. Na kuma sayi gidanne a hanun wani mutum Ibrahim Askari”. Abu Zainab zai sake magana Kaka ya girgiza masa kai alamar kar yace komai. Godiya sukai masa da sallama suka wuce. “Baba ban san miyasa ka dakatar dani ba. Dama zan tambayesa ne ko zai faɗa mana inda zamu samu shi Ibrahim Askari ɗinne”. Numfashi Kaka yaja ya fesar, “Dalilin da yasa na dakatar da kai kenan. Kasan shi al'amari irin wannan yana buƙatar kasan dawa zakai maganar abu na gaba. Inaji a jikina waɗanda suka haddasa tushen wannan matsalar dole suma zasu kasance suna bin bayanmu domin toshe duk wata hanyar da zamu iya bi. Dalili kuwa shine ina kallon lauje ne cikin naɗi akan al'amarin”. “Eh gaskiya hakane kuma Baba. To amma in har hakane mizai hana mu nema lauya, sai nake ganin cikin sauƙi shi zai iya binciko mana inda suke ma, kuma koma minene sai yazo cikin sauƙi tunda ana magana ne akan abinda ya shafi shari'a ko kuwa?”. “Itama wannan babbar shawara ce a mahangar hankali Zakariyya, sai dai shi lauyan ne matsala musanma irin mu wanda muke bukata. Mai gaskiya da amana”. “In dai dan wannan ne babu damuwa insha ALLAHU, akwai yayan matata data rasu, kwararren lauyane kuma mai nagarta da nasan zakaso aikinsa kuma zai taimakemu kasancewarsa babba. A yanzu dai nasan bazamu samesa a gidansa ba. Bara kawai muje ofishinsa”... ★★..... ★... ★★..... Kamar yanda Iffan ta nema alfarma a wajen Daneen Ammarah akan ɗakko mata akwatinta da aka kawo ta gidan dashi ya iso gareta. Taji matuƙar sanyi a ranta da farin ciki. Hadimar data kawo na fita ta buɗe akwatin ta shiga dubawa. Alhamdullah komai yana nan yanda yake, hatta takardar da malam Fawzan ya bata ɗinnan itama tana a inda ta ɓoye ta. Tana idar da sallar azhar littafin data sako a kayan nata kawai ta ɗauka da biro ta fara rubutu. Anutse take rubuta komai daya faru daki-daki tun daga barowarta gida har zuwa shigowarta cikin masarautar, abinda ya faru da ita dama wanda ke kan faruwa bayan warkewarta. Da zarar taji motsi koda ma Daneen Ammarah ne sai ta boye, a haka ta kwashe kaf yinin har zuwa dare tana abu ɗaya. Da daddare bayan kammala shirin barci maimakon kwanciya zaman karatun Alkur'ani tayi, koda Daneen Ammarah ta shigo ta sameta a hakan bata katseta ba. Tasa Hadimar dake biye da ita ajiye mata madarar da suka shigo da ita. Daga haka ta fice taja mata ƙofar da nufin ta dawo zuwa anjima, dan yanzu tana son zuwa ta duba Malikat Haseena ne da yai batajin daɗi. Iffah na ganin ta fice ta sauke ajiyar zuciya, addu'a tai ta rufe Alkur'anin ta mike, kofar taje ta sanyama key bayan ta leƙa babu kowa a corridor ɗin. Ta ɗan jingina da ƙofar tana mai ambaton “Alhamdullah” da sakin ɓoyayyen murmushi. Cikin sassarfa tabar jikin ƙofar zuwa ga akwatinta, ta buɗe tare da ɗakko wayar Arfa da takardar da Malam Fawzan ya bata. Number da aka rubuta ta kwashe a wayar, ta haye tsakkiyar gadon ta kwanta tare da jan lallausan bargon ta shige ciki har kanta sannan tai dailing number. Gaba ɗaya a kage take da zumuɗin a ɗauka. Dan haka take bin sautin shigar kiran da zuciyarta. Sai dai harta yanke ba'a ɗaga ɗin ba. Kira ta sake yi, nan ma dai shiru, bata gajiya ba ta cigaba da kira har fin sau goma kafin a ɗaga a karo kusan na goma sha biyar. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tamkar wadda aka tsamo daga cikin ƙanƙara. Sai kuma tai saurin faɗin, “Assalamu alaikum”. “Wa'ake nema?”. Aka faɗa daga can maimakon amsa sallamar tata. Da lafiya lafiya ne sai tayi mitar ƙin amsa sallamar, amma sai tai saurin faɗin, “Sir Ajmaal”. “Wa'ake nema?”. Aka sake maimaita mata tambayar. Zuciyarta ta ɗan fara zabura amma sai ta danne ta sake maimaitawa itama. “Sir Ajmaal”. “Wa'ake nema?”. Still aka sake faɗa kamar dai ba'ama jita ba. Wayar ta janye a kunenta ta tashi zaune ta ɗauka takardar, number dai dake a jikice dai-dai batai mistake ba. Sake maida wayar tai kunne aranta tana faɗin (bara naga ƙarshen ku dai) ta sake amsawa da “Sir Ajmaal”. “Kin saɓa lamba”. Aka bata amsa da yanke wayar lokaci guda batare da anjira cewar ta ba...... ★★..... ★... ★★..... Kasancewar Abu Zainab suruki ga barrister cikin sauƙi suka samu ganinsa ta hanyar kiran waya. Har office yasa masinjansa daya fita yay musu iso ya shiga da su. Ganin lafiyayyen office ɗin nasa dama hukumar tasu ya sake tabbatar ma da Kaka babbane gaskiya. Sun gaisa cikin nuna sanayya shi da Abu Zainab. Ya kuma gaida Kaka da girmamawa kasancewar tsoho dama zai iya haifarsa. Basu saurari lemo da aka kawo musu ba Abu Zainab ya shiga masa bayani dalla-dalla. Sai da ya gama tsaf Barrister Abdallah dake rubuta wa ya ajiye biron yana jinjina kansa. Kaka ya fuskanta cikin son ƙarin bayani.... “Baba kaima kasan shi Dawood ɗin kenan?”. “Tabbas na sanshi yaro. Hasalima ga gidan mahaifin shi Muhammad Zayyanu gana mahaifin Dawood. Sannan ta ɓangaren mahaifiyata ma munada alaƙar jini da mahaifin nasa. Shine kuma yay sanadin zuwan Muhammad Zayyanu garin nan, shi kuma Muhammad Zayyanu ya koya masa noman zuma daya gada ga mahaifinsa”. “Eh lallai sanayya ce babba kam. Sai dai kuma inaga ya kamata nasan miya rabasu? Dan yanzu hujjojin hanunmu sune zasu taimaka mana wajen kubutar da su saboda wannan case ne babba kuma da alama shiryayye” “To nidai kai tsaye banace ga abinda ya zama sanadin rabuwar kawunan nasu ba. Dan shi Muhammad Zayyanu mutum ne mai zurfin ciki da rashin kwaramniya. Amma dai lokacin da naga bana ganinsu tare na tambayesa ko akwai matsala? Shi da abokin nasa. Sai ya sanar min shi dai a saninsa bai masa komai ba ya janye daga jikinsa, ya kuma bisa ya bisa babu adadi danya faɗa masa amma yaƙi, daga karshe ma ya tattare kayansa da iyalinsa sukabar anguwar, bai kuma sake ganinsa ba har watanni sunja a lokacin. Na bashi shawarar ya ƙara nemansa dai, da muka sake haɗuwa na tambayesa sai yace ai yama bincika yabar gari. Iyakar abinda na sani kenan gaskiya”. “Shi kuma Dawood ɗin baka sake ganinsa ba kaima?”. “Eh to gaskiya ban sake ganinsa ba. Dan ko'a rasuwar mahaifinsa sai wai-wai mukaji yazo yay gaisuwa ya tafi kawai. Daga nan kuma dai bamu sake jin ɗuriyar tasa ba dan dama mahaifiyarsa bata raye tuni”. Barrister dake faman kaɗa kai ya sake ajiye bironsa. “Uhhm yanzu to inaga mataki na biyu shine musan wane station suke. Ko kuma inda ita matar tasa take”. Cikin damuwa Abu Zainab yace, “Munje inda muke tunanin samun nata bamu sameta ba. Sai dai an ambata mana sunan wanda ya saida gidan ga wanda ke ciki yanzu”. “Miye sunan”. “Ibrahim Askari”. “Badamuwa kuje abunku, insha ALLAHU daga nan zuwa gobe za'a nema mana Ibrahim Askari ɗin. Suma kuma zan ɗan bincika ta hanyar jami'an dana sani a mabanbanta station na garin nan”. Sosai kaka ya dinga ma barrister godiya. Hakama Abu Zainab. Shi dai faɗa musu yake karsu damu. Aje a cigaba da addu'a komai zai zama labari insha ALLAHU...... ★★..... ★★.... ★★..... Iffah kamar zatai kuka ta ƙara dailing number amma sai ma aka sanar mata switch up. Wani irin zafi da lugude ƙirjinta ya shiga yi, ta shiga neman number Malam Fawzan cikin rawar jiki tunda dai shine ya bata number..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_23_* ........Itama ɗin dai switch up. Wasu zafafan hawaye suka silalo a kumatun ta. Ƙoƙarin sake kiran waccan number ta gwadayi knoking ƙofar da akai ya katseta. Da sauri ta yanke kiran da kashe wayar ma baki ɗaya ta ɗaga gadon ta tusasu har da takardar gaba ɗaya sannan ta sauka dan tasan bazai wuce Daneen Ammarah ba... “Ibnati baki barci ba kenan?”. Kan Iffah a ƙasa tai ɗan murmushi. “Yanzu zanyi Mamy karatu na kammala”. “Masha ALLAH, ya kamata ki kwanta to dare yaja, nima zuwa zanje na kwanta”. “To Mamy ALLAH ya tashemu lafiya”. Koda Daneen Ammarah ta wuce Iffah ba kwanciyar tai ba, sake ɗakko wayar tayi ta cigaba da neman wancan layin da a yanzu ake cemata not available saɓanin switch up na ɗazun. Hakama number Malam Fawzan har yanzun. Daga ƙarshe dai barci ɓarawo gwanin iya sata ne ya saceta akan dole ta haƙura, sai da asuba ta tsinta wayar a ƙasa yashe.... Yau dai kam ta ƙudiri niyyar fita gaida tsohuwa Malikat Haseena da kanta, tunda dai jikinta Alhamdullah hatta saɓar ma sai inda ba'a rasa bane bai gama ba. Bayan hadimar dake gyara ɗakin ta kammala ta fita key ta sama ƙofar sannan ta shiga wanka. Dan duk da tausayin hadiman da takeji a yanzu batajin zata sake yarda da waninsu. Ta fito tana tsaka da shiryawa cikin ɗaya daga kayanta na gida akai knoking. Karasa saka abayar tayi sannan taje ta buɗe, a tare suka sakarma juna murmushi, tai ƙasa da kanta tana faɗin, “Barka da safiya Mamy”. Daneen Ammarah takai hannu ta taɓa kanta da faɗin, “Kin tashi lafiya?”. “Alhamdullah”. “Haka ake so. Ga kayanki nan na amfanin yau, mun zaɓi yin hakane saboda gudun abinda zai iya zuwa ya dawo Ibnati, amma insha ALLAH kayanki na amfani na gab da kammaluwa, saiki shirya ni zanje sashen Umm Jasrah. Ki tabbatar kinci abinci sosai yanzu zan dawo ba jimawa zanyi ba”. “Adawo lafiya Mamy a gaisheta”. “Zataji, amma ki tabbatar kin canja waɗan nan kayan”. Kai kawai Iffah ta jinjina mata. Amma a ranta tana mamakin minene aibun abayar tata? Tana cikin sabbin kayantama da take matuƙar ji da su. Shigowar hadimai biyu da kayayyaki ya katse mata mitar tata, sai dai batace komai ba bayan amsa musu gaisuwa. Fita ɗayar tai aka barta da wadda tafi yawan kasancewa da ita, tazo gabanta ta zube kanta a rissine. “Ya Zawjata-almilki bisa umarninki za'a shirya kayan”. Karo na biyu Iffah ta amsa neman izini da umarni ga hadimai a gidan. “Ba yanzu ba, zaki mun rakkiya ga Mamma ne, ki jirani a waje”. “Umarninki shi nake zaman jira ya Zawjata-almilki”. Hadimar na fita ta taka inda kayan suke tana dubawa. Tunda ta samu lafiya kullum da safe za'a kawo mata kaya kala uku, washe gari za'a kwashesu koda daya kawai ta saka a sake ajiye mata wasu. Da farko ta ɗauka ko haka tsarin masarautar yake. Sai a yau bayanin Daneen Ammarah yasa ta fahimci ita akema hakan saboda tsaro. Waɗanda ranta yafi kwantawa da su ta dauka ta saka. Ta koyi ƙyau sosai musamman da suka kasance bakake da adon stones masu sheƙi da ɗaukar idanu. Ga farar fatarta data koma ja ƙaɗan saboda saɓar datai tamkar ta larabawa ta sake fitowa. Ɓoyayyun turarenta na wajen Kaka ta ɗakko ta saka, wani irin ƙamshi mai daɗi da saka zuciya nutsuwa ya fara ratsa ɗakin... Sosai murmushi ya bayyana a fuskar tsohuwa Malikat Haseena saboda ganin Iffah akan kafafunta, takuma ji daɗin wannan ziyarar bazata data kawo mata duk da kuwa suna a sashe ɗaya ne. Iffah data kai zaune gefenta bisa tattausar dardumar da aka ƙawata falon da shi ta risinar da kai tana gaisheta da tambayarta yaya jiki?. “Alhamdullahi ƴar albarka. Yaya naki jikin?”. Malikat Haseena ta amsa da kulawa har yanzu murmushi ƙawace da fuskarta. “Naji sauƙi ai Mamma” (kamar yanda taji Daneen Ammarah na kiranta. “To Alhamdullah ALLAH ya ƙara kiyaye gaba”. Da amin duk hadiman wajen suka amsa. Malikat Haseena sallamar duk Hadiman tayi, tare da bada umarnin a shirya mata breakfast da Iffah. Hakan ya bama hadiman mamaki sosai, dan duk wanda Malikat Haseena zata buƙaci zaman cin abinci da shi ba karamin mai sa'a bane ba. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa aka kammala shirya komai, ita dai Iffah na kallon ikon ALLAH da tsagwaron mulki wajen wannan tsohuwa. A ranta kam tunani take shin wai idan haka matan suke waishi babban dodon nasu yaya za'a gansa kenan?. Bisa umarnin Malikat Haseena Iffah ta mike suka nufi wajen da aka shirya abincin. Zamansu dai-dai da shigowar amintacciyar hadimar Malikat ɗin ɗauke da wani ƙaramin kwano... Shigar ƙamshin turaren Iffah hancin Hadima Banou ya saka jikinta fara tsuma. Hanunta na ɗan rawa ta sunkiya zata ajiye kwanon suka haɗa ido da Iffah. Zabura tayi da sauri ta miƙe kanta a sunkuye. Iffah ma dake jin jikinta na wani irin yamutsawa ta sake kallonta da kyau, haka kawai matar batai mata ba, gata wata irin doguwar mace gandaƙaiƙai kamar namiji babu wani fasalin mata tattare da ita... Malikat Haseena da rawar jikin Hadimar ya bata mamaki itama ta tsura mata idanu. Sai dai mulki da kasaita baisa ta tanka ba. Hadima Banou dake jin kamar ta zura a guje saboda yanda take jin jikinta ta zube ƙasa, cikin rawar hannu ta fara yunƙurin haɗama Malikat Haseena abinci.. Iffah dake mata kallon nazari ta dakatar da ita. “Kinga jeki kawai”. Ai kafin ma ta rufe baki tuni ta mike zaram kamar wadda ke akan wuta. Iffah da gaba ɗaya abin ya gama ɗaure kanta ta fara haɗama Malikat Haseena abincin da kanta. Itako Malikat Haseena komai bata kawo a ranta ba game da yanayin Amintacciyar hadimar tata, saboda takan ganta a wasu yanayi daya fima hakan, dan haka ta jima da sakata a jerin masu aljanu... Hadima Banou na fita a falon ta sauke wani irin nannauyar ajiyar zuciya da kai hannu ta yarce gumin dayay sharkaf a goshinta kamar wadda ta tiƙi surfen gero. Gaba ɗaya manyan idanunta masu saka tsigar jikin mutane tashi sunyi jazur. Gefe ta koma ta zauna a ranta tana fatan ALLAH yasa har Iffah ta tafi Malikat Haseena bazata nemeta ba. A ganinta ma tai zamanta anan koda an nemetan ai sai an ganta. Wannan shawarar data yankema ranta ya sata cigaba da zama a wajen har lokacin jikinta bai gama komawa dai-dai ba.... Gaba ɗaya Iffah kasa sakewa taci abincin tai saboda kunya, ganin haka cikin hikima Malikat Haseena ta cigaba da ɗan jan ta da hira domin jan ra'ayinta, itako tana amsa mata a kunyace da tsakurar abincin. Suna a haka Daneen Ammarah ta shigo, itama dai ta nuna jin daɗinta na ganin Iffah ɗin tare da jin kaunarrta har cikin rai. Zama tai itama aka ɗora cin abincin da ita suna yar hira jefe-jefi da Malikat Haseena. Iffahn dai nata saurare kawai, sai kuma murmushi. Rabin hankalinta kam nacan wajen tunanin hadima banou da yanayin ta.... ★★.... ★.. ★★.... Kamar yanda Barrister yayma su kaka alƙawari ya samo Ibrahim Askari ta hanyar mutumin nan da suka fara zuwa wajensa. Fuskarsa cike da murmushi yake dubansu, dan tun yana can ya sanarma Abu Zainab su haɗu a office. Sai gashi kafin ya iso ma su har sun iso. Ko cikakkiyar gaisuwa basuyi ba ya fara musu bayani. “Alhamdulh an samo Ibrahim Askari, ya kuma bani cikakken adireshin Dawood ɗin, hasalima yace shiyya sayar masa da gidan daya koma ɗin. Ga adireshin gidan ya bani”. Sosai farin ciki ya bayyana a fuskar Kaka. Ya dinga jerama Barrister addu'a da fatan alkairi. Shima dai Abu Zainab yayi masa godiya, tare da ɗorawa da faɗin, “Barrister yanzu mune zamuje can ɗin? Kokuwa kai ne?”. “Mu duka babu wanda zai je Zakariyya”. Kallonsa sukai su duka, ya jinjina musu kansa da buɗe wani littafi a gefensa ya yago takarda, ɗan rubutu yay da sake ɗagowa ya dubesu. “Kamar yanda na faɗa muku mu duka babu wanda zaije. Domin ita Shari'a takanzo saɓanin hankali. Sannan bamu san nasu shiri ba, zasu iya amfani da duk wani yunkurinmu a yanzu. Dan haka nayi abinda ya dace bayan barina wajen Ibrahim Askari. Akwai wani babban police dana sani kai tsaye naje garesa, nakumayi sa'asar samunsa. Nayi magana dashi da rokonsa ya bincika mana inda zamu iya samun su, Alhamdullah kuma ya amsa, yanzu haka kiransa nake jira kamar yanda yaymin alkawarin kafin cikar awa ɗaya”. Anan ɗin ma dai farin ciki ne a fuskokin su Kaka, sai faman sauke ajiyar zuciya sukeyi..... ★... ★★.... ★.... Zamu iya cewa gaba ɗaya yinin yau Iffah ta kare shine a neman number Malaminta Fawzan da abokinsa Ajmaal. Amma abin mamaki har yamma amsa ɗaya ce layukansu not available. Gaba ɗaya tayi firingai-firingai na damuwa, duk yanda take ƙoƙarin ɓoyewa da danne hawayenta sai da suka zubo bayan ta idar da salla. Bakomai yasata shiga damuwar akan son samunsu ba sai rashin samun number Babiy da Hanash da batai ba suma. Tana son jin wani abu game da ahalinta, dan yawan faduwar gaban da take da mummunan mafarki yasa tanaji a jikinta akwai matsala. Tama rasa wane tunani zatayi, har text message ta turama Malam Fawzan akan ya taimaketa ya duba mata iyayenta amma shiru kakeji, bama tada tabbacin ya gani ko bai gani ba. Kuka taci sosai a wajen kafin ta mike tana share hawaye bisa shawarar zuciyarta. Wayar ta sake ɗauka ta sake tura sakon data turama Malam Fawzan a layin Ajmaal abokin nasa. Tana fatan ɗaya daga cikinsu yaga saƙon koda bata samu sauran biyan bukatarta ba. Jikin window ta koma ta tsaya tana mai shaƙar iskar dake busowa mai daɗi, kamar ance kalla gefe ta hango Hadima Banou can jikin filawoyin saitin ɗakin Malikat Haseena tsugunne kamar tana tona rami, sai faman waige-waige take alamar rashin gaskiya. Da farko tsura mata idanu Iffah tai, sai kuma ta zabura bisa umarnin zuciyarta. Sai da ta tabbatar wani baiga sanda ta fito a dakinta ba sannan ta fice, kasancewar ta naɗe har fuskarta da ɗan kwalin abayar jikinta yasa babu wanda ya ganeta, balle abayar jikin nata ɗaya daga cikin natane na gida data canja bayan barowarta wajen Malikat Haseena. Da ƙyar ta gane hanyar dazata ɓulla bayan, dai-dai Hadima Banou na ƙoƙarin maida kasar data tone alamar harta saka abinda zata saka. Sauri-sauri takeyi harta kammala, ta ɗago da nufin barin wajen taja ta tsaya a kiɗime ganin mutum tsaye a bayanta. Amma kasancewar ta mai shegen tsurin ido sai ta dake a zahiri tana kallon Iffah da har yanzu bata janye mayafin data yane har fuskar ba.... “K! Ubanwa ya kawoki nan?”. Ta faɗa da zaton cikin hadimai ne irinta. A hankali iffah ta karasa takowa gabanta, tare da janye mayafin ta saka idanunta cikin nata jajaye marasa ƙyan gani. Sosai hadima banou ta rikice har rawar jikinta ya bayyana. Iffah ta janye idanunta daga kanta ta maida akan ramin, “Mi kika binne?”. “Ranki ya daɗe babu komai, w... W... Wani magani ne kawai da nake son yin amfani da shi.....” “.....Shine kika shuka shi anan cikin rashin gaskiya? Wacece ke? Mi kike kullawa”. Tambayoyin sunma Banou yawa da tsauri wajen bada amsa, a take ta sake gigicewa duk da tana ƙoƙarin ƙirƙirar jarumtar dole. Wuceta Iffah tai zuwa wajen ramin, ta tsugunna da daukar iccen datai tonan da shi ta shiga sake tone kasar da Bismillah. Firrr wani abu kamar tsintsuwa ya fito a ramin yay sama. Iffah ta mike da sauri ta bisa da kallo harya bace. Juyawa tai da sauri inda Banou take, dai-dai ko tayi shirin silalewa tabar wajen ta dakatar da ita. Ƙasa tai da kanta jikinta na matukar rawa, Iffah ta kare mata kallo sama da kasa na wasu sakkani, sai kuma ta girgiza kai. “Wani asirinne haka bizne tsuntsuwa da ranta saboda son zuciya? Ko wani ya sakaki biznewar saboda ya isa? Kokuwa ke ɗin kina a cikin jinsin Mayu ne? Dan a cikin ukun nan dana lissafa dole ne a samu ɗaya tattare da ke tsohuwa”. Kuka Banou ta fashe da shi gwuyawunta a ƙasa. “Ranki ya daɗe ban fahimci abinda kike nufi ba, nifa magani na shuka ki yarda dani”. “Uhhm wato magani kika shuka, tsohuwa kalleni da kyau ki ganni banyi kama da wanda akema rufa ido ba, amma zan baki lokaci kije, zan nemeki a lokacin daya dace. Idan kika hangi gudu baki da wajen iya ɓoye min, idan cutar dani ne zagaye nake da kariyar UBANGIJINA, idan yunkurin salwantar da rayuwarkine idona biye yake dake tako ina. Shawara ya rage gamai shiga rijiya”. Da wani irin mummunan kallo hadima banou tabi bayanta da shi, ta cije baki da rumtse jajayen idanunta da karfi.........✍️ 🤔 Wannan ƴa ta Babiy ƙarfin halinta da tarar aradu sun mata yawa. Dole dai sai ta kai kanta inda za'a lamushete oh ni Balki😜. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_24_* ..........Komai daya faru tsakanin Iffah da Hadima Banou akan idon Daneen Ammarah ne, dan itama tayi yunƙurin fitowar ne ganin Banou na tono a bayan windown Mamman sai ta hango Iffah na tahowa. Kasancewar ta ganta da rigar jikinta a ɗazun yasa kai tsaye ta ganeta. Da farko gabantane ya fara faɗuwa da tunani iri-iri, shiyyasa ta tsaya domin ganema idanunta. Sai dai kalaman Iffah da yanayin Hadima Banou ɗin ya sata shiga ruɗanin tunani. Idan har zata auna da hankalinta matsayin babba itama Iffah taga Hadima Banou ne shiyyasa ta fito, a yanayin Banou kuma ya nuna akwai wani ɓoyayyen al'amari na rashin gaskiya tattare da ita. To amma su maiyasa a tsahon shekaru basu taɓa ganin wannan fuskar ta Banou ɗin ba? Wacece Iffah? Anya kuwa ba akwai abinda ya kamata ta sani dangane da yarinyar nan ba?...... ★Iffah da al'amarin wannan masarauta ya fara ruɗama tunani tana shiga ɗakin dake matsayin nata yanzu ta murza key. A jikin ƙofar ta jingina da lumshe idanunta tana sauke numfashi. Ita kanta taga ƙarfin halinta yau, dan zata iya rantsewa bata san a ina ta samo wannan jarumtar ba. Idanun ta buɗe tare da riƙe ƙugu ta karyar da kai alamar nazari. In fa har ta canka dai-dai tabbas wannan hadimar mayya ce. Dan bata manta da wani labari da Iyyani ta taɓa basu ba na mayya yar Danƙo datai zamani a kauyen jumna shekarun baya. Babu banbanci da abinda taga matar nan tayi yanzu, dan da alama kurwar wani ta laso tazo ta boye a wajen. “Bahun ubancan, eh da gaske dai ashe lamushe ƴaƴan mutane ake a masarautar nan tunda ga alama harda su bayi an barbaɗa musu muguwar tambaya. Shi baƙin babban dodon nasu nacinye mutanen gari su kuma bayi nacinye junansu a cikin gida”. Tai maganar a fili cikin ƙankance idanu na alamar tunzuruwa... Murmushi Daneen Ammarah dake bakin ƙofa tsaye ta saki, dan nutsuwar da zuciyarta ta kasa mata ya sata biyo bayan Iffah, har ta kai hannu zatai knoking sai kuma ta fasa da tunanin inhar Iffah nada wani mugun nufi a kansu to baro can zata samu wani abun take aikatawa a yanzu. Dan haka ta ɗan kara kunenta kaɗan jikin ƙofar, cikin Sa'a kuwa ta jiyo mi Iffah ta faɗa saboda yanda tai maganar da ɗan zafi sai ta fita da ɗan karfi kaɗan. Ƙofar ta fasa bugawa ta koma ɗakinta da baya. Itama dai ƙofar tata ta sanyama key duk da tasan babu wanda zai shigo mata. Kai tsaye wadrob ɗin ta ta nufa, a cikin wani akwatin ƙarfe karami mai ƙyau ta fiddo waya bayan ta danna madannan sirri ya buɗe. Wayar ta shiga ƙoƙarin kunnawa tana mai rufo windows ɗin ɗakin nata. Sai da tai danne-danne kusan na mintuna biyu alamar text ta tura. Kira ne ya shigo, sai a ring ɗin karshe ta ɗaga, batare da jiran wani gaisuwa daga wancan ba cikin bada umarni tace, “Daga yanzu zuwa safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu ina buƙatar sanin komai akan Zawjata-almilk ta uku. Idan nace komai yana nufin komai da komai”. Kitt ta yanke kiran tana wani irin murmushi tun kan ma ta samu amsar data bukaci sani. Wayar ta kashe gaba ɗaya ta sake maidata inda ta dakkota...... (🤔Wai su kowa da tasa manufar ne????) *_MALIKAT BUSHIRAT_* Zaune take hakimce kamar ko yaushe cikin kwalliya mai matukar ɗaukar idanu. Ga wani sihirtaccen ƙamshi mai ratsa zuciyar duk wani mai shaƙa na tashi. Shi kansa falon kamshinsa na musamman ne. Gefenta na dama Jasrah ce itama cikin kwalliyar, zuwanta kenan sashen sakamakon aiken data samu daga ƴar uwar tata. (Itama dai Jasrah anan cikin masarautar take aure, tana kuma auren ƙanin marigayi Tajwar Haysam ne da suke uba ɗaya. Dan kamar yanda Tajwar Haysam suke su huɗu a ɗakinsu suna kuma da ƴan uba har su kusan tara, sai dai mata sunfi yawa a ciki. Su tarannan kuma ƴaƴan mata uku ne. Mijin Jasrah shine babba a cikin ƴaƴan amaryar Tajwar Haysam da ake kira Ameera Aasfah a masarautar. Mace ce mai kirki da sanin ya kamata, jininsu kuma yay matuƙar haɗuwa da Malikat Haseena. Dan idan ka gansu bazaka taɓa ɗauka kishiyoyi bane a sanda tana raye. Yaranta biyune ita kacal, Miran Arshaan shine babba, shine kuma ɗa na takwas a wajen Tajwar Abdul-majeed, a maza kuma na uku, shine mijin Jasrah a yanzu, sai ƙanwarsa Daneen Fu'ada, a yanzu haka tana aure itama. Ƙaunar dake tsakanin Malikat Haseena da Ameera Aasfah yasa shaƙuwa sosai a tsakanin ƴaƴansu, hakan yasa Tajwar Haysam ke kallon Miran Arshaan tamkar ƙaninsa Miran Nayyar daya rasa, shine ma da kansa ya aura masa Jasrah. Wannan kenan, ALLAH yasa kun gane🥱). “Akia kince nazo amma kin kasa cewa komai? Wani abun ya sake faruwa ne?”. Numfashi Malikat Bushirat ta sauke a hankali tana kallon ƴar uwar tata da takema kallo tamkar first born ɗin ta. Kamar bazatai magana ba sai kuma ta nisa cike da kasaita. “Komai bai sake faruwa ba, sai dai ina gudun sake faruwar. Sanin kanki ne Jasrah ba lallai kosu waye su haƙura ba dan yarinyar nan ta kuɓuta a yanzun, sannan ma bayan ita akwai sauran yaran biyu da har yanzu fargaba ta hanamu kaisu turakar Saifulmalik. Kin san kuma rashin kai su zuwa nan da ɗan lokaci sai kinji an fara kace-nace”. “Hakane Akia. Amma ke mikike son cewa?”. “Zancen dai ɗaya ne shine inajin tsoro, na biyu kuma da gaske yarinyar nan ta shiga raina fiye da duk matan da aka kawo gidan nan matsayin Zawjata-almilk”. “Wlhy nima har cikin rai yarinyar ta shiga raina. Gata da tarbiyya daga ganinta, sannan itace mafi ƙanƙanta a duk matan na Son”. “Wannan yana ɗaya daga cikin abinda ya sake jan hankalina a kanta Jasrah, shiyyasa yanzu da wani tunani yazo min nace bara nai shawara da ke. Shin kina ganin naima Mamma (Malikat Haseena) magana gobe idan ALLAH ya kaimu da Saifulmalik zaije gaisheta a kusanta shi da yarinyar nan suga juna? Sai nake ganin hakan zai canja wani babban al'amari da masu mana yankan baya ke ƙullawa. Tunda kinga dai duk matansa sai an kaisu turaka yake da damar ganinsu kamar yanda kowa yasan dokar kenan ga duk Zawjata-almilk tun ƙarnin baya”. “Eh gaskiya kuma wannan tunani ne mai ƙyau Akia inhar Mamma zata amince ɗin. Dan Kinga muma a karan kammu wata hanya ce da zamu fuskanci wani abu akan shi kansa..” “Wannan gaskiya ne. Dan da gaske Jasrah a yanzu har shi kansa zuciyata rawa take ga al'amarinsa, dan abinda ke faruwa dole ne kowa ya zama abin zargi har mu kammu, ke nama takaice miki zance ni kaina yanzu ban yarda da kaina ba”. Murmushi Jasrah tai har haƙoranta na bayyana. Tace, “Kai Akia kinada abin dariya wlhy wani lokacin. To inke baki yarda da kanki ba mu kuma dawa zamu yarda kenan?. Kawai dai inaji a jikina koma minene ya kusa zuwa ƙarshe ta silar yarinyar nan tunda har ALLAH ya fara nuna musu iyakarsu suka gaza cin nasara a harin farko da suka kai mata. Yanzu dai bamu da lokaci, ki tattauna da Mamma ɗin kawai. Hukuncin data yanke sai mu karɓa kawai”. Malikat Bushirat ta jinjina kai kaunar ƴar uwar tata na sake ratsata. Koba komai idan ta tattauna da ita takanji sanyi a ranta....... ★★.... ★.... ★★..... “Wai nikam ɗazu ina ƙoƙarin shiga fada naga kamar motarki ta gitta, kinje wani waje ne?”. Shayin da take ƙoƙarin zuba masa ta karasa tare da miƙa masa. Sai da ya amsa ta koma ta zauna tana mai ɗan ɗage kafaɗunta. “Kaima kasan fita ta bata wuce wajen Akia ai Abu Harith, wlhy itace fa tai min kiran gaggawa shine ka ganni na fitan. Amma lafiya kuwa har irin wannan lokacin kuna a fada?”. “Uhm to lafiya lau za'ace, anyi baƙin bazata ne kawai ga Shahan-shan ya rigada ya shige kuma. Dole mu mukai zaman tarbarsu. Amma kiran gaggawa wata matsalar ne ta sake faruwa? Ko jikin Zawjata-almilk ɗinne dai?”. “No akan dai wadda ake cikine. Jikinta kuma Alhamdullah, idan ma ka ganta yanzu bazakace wani abu ya faru ba. Kawai dai Akia ce ke ganin ya kamata idan Shahan-shan yaje gaida Mamma gobe idan ALLAH ya kaimu Zawjata-almilk ta ziyarcesa ko hakan zai kawo wani sauyi kan abinda har yanzu muka kasa sanin kansa”. “Amma baƙwa ganin hakan wani ganganci ne? Sannan dokace fa Shahan-shan baya ganin matansa sai a turaka”. “Eh muma mun duba wannan ɗin, dan haka ma bamu wani yanke shawara ba akace sai an sanarma Mamma. Amma kai ya kake gani akan hakan. Abu Harith wlhy Akia na bani tausayi matuƙa, a yanzu har takai da kanta itama zarginsa take shi yake ɓarnar nan”. “Ya ALLAH wannan wace irin magana ce haka? Miyasa zatai irin wannan tunanin akan ɗanta. Bana jin Eshaan zai taɓa aikata makamancin hakan. Kawai dai akwai abinda yake ba daidai ba”. “Sosai kuwa. Amma insha ALLAHU ta sanadin yarinyar nan kowa sai yaci ƙaniyarsa. Dan haka kawai nakeji a jikina ita ɗin haske ce a wannan daula. Tunda har gashi ta karya tarihin farko na azzalumai”. “Haka muke fata, dan muma an tattauna akan hakan sosai jiya da yau a fada. Kusanma issue ɗin da ake kai kenan kawai yanzu a majalissa. Sai na kisan hadiman can”. “To ALLAH ya dafa mana mu da ku, ya kaimu ranar da zamu ga iyakar wannan al'amari”. “Amin my meera”. Yay maganar da wani salon kashe ido mai cike da soyayya da kaunarta. Murmushi tayi itama tana miƙewa, “Bara na kimtsa kafin ka kammala ko”. Kai ya gyaɗa mata idanunsa narke a kanta.. Tana juya baya ya bita da wani irin matsiyacin kallo mai ma'anoni da yawan gaske yana tsuke fuska da jan tsaki...... 🤦Jasrah kamar yanda ƴar uwarki ta faɗa miki kowa ba abin yarda bane yanzu🧐. ★★.... ★★..... Kamar yanda Malikat Bushirat suka tattauna da Jasrah batai ƙasa a gwiwa ba tana idar da sallar asuba ta fita daga sashenta cikin badda kama zuwa sashen Malikat Haseena. Kasancewar ta sanarma Daneen Ammarah tare suka nufi ɗakin Malikat Haseena ɗin. Itama tasan da zuwan Malikat Bushirat ɗin. Dan haka basu ɓata lokaci ba suka fara tattaunawa dan ta samu ta koma kafin gari yay haske. Da farko dai malikat Haseena ta kakkawo musu dokokin masarautar masu tsari dangane da haɗa Shahan-shan da Zawjata-almilk kai tsaye ba'a turakarsa ba. Sai dai bayanin da sukai mata da nusar da ita abinda suke son tabbatarwa yasa itama ta amince. Sai dai da sharaɗin komi ya biyo bayan hakan laifinsu zata gani. Cike da yaƙinin fatan karma wani abu ya faru suka amince. Dan haka tai musu sallama ta koma. Daneen Ammarah da tunaninta nada banbanci da na Malikat Bushirat akan wannan haɗuwa tai murmushi a ranta tana mai addu'ar samun nasara. Domin wannan yaƙi kamar natane ita kaɗai sakamakon itace kawai tasan ɓoyayyen sirrin daba kowa ya sani ba sai UBANGIJIN talikai. Fatanta shine komai yazam yana gangarowane ga faɗan karshe akan maƙiya koda ita zata rasa rayuwartane a yayin gumurzun... (Daneen Ammarah kin fara bani tsoro fa🧐😞). *_SHAHAN-SHAN_* Yau ɗin ce dai ta kasance rana da yake zuwa gaishe da kakarsa Malikat Haseenah. Irin wannan rana kuma tana zuwane sau ɗaya a kowanne wata. Sai dai idan ita ke buƙatar ganinsa ta samesa a sashensa. Amma a kowane wata yanada ranaku biyu na ziyartar kakar tasa da mahaifiyarsa. Malikat Haseena yake fara dubawa a farkon wata, Malikat Bushirat a tsakkiyar wata. Duk da fitace ta dare da ba lallai kowa ya gansa ba ya kasance cikin shiri mai ɓoye ainahinsa, ga wani ƙamshi na isassun da suka isa na tashi tattare da shi. Takunsa da ƙarfin izzarsa ya isa tabbatar maka eh lallai Shahan-shan ne da kansa. Ƙasaita jinin jikinsa ce, kamewa da isa adonsa ce, kwarjini da nutsuwa halittarsa ce.... Duk da farkon dare ne dan kwata-kwata ƙarfe takwas ne, amma masarautar tayi tsit kowa ya nutsu a inda ya dace saboda sanin wannan rana ce da Shahan-shan ke fitowa zuwa sashen Malikat Bushirat. Babu wani Hadimi dake kai kawo sai Ghazi da masu tsaro da suka tsare ko'ina fiye da kullum. Hakama sauran jama'a in ba babba mai faɗa aji ba babu wanda keda hurumin wani kaikawo a irin wannan daren dake zuwa a wannan rana saboda fitowar Shahan-shan...........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_25_* .......Turus Jasrah tayi ganin babu Abu Harith a inda ta barsa. Sai kuma ta nufi ɗakin barcinsa da tunanin koya shige. Nan ɗin ma dai babu alamarsa har cikin bathroom. Batare data kawo komai a ranta ba ta ɗan ɗage kafaɗa ta fito. ★Shi kuwa da tun bayan ficewarta ta ɗazun da kamar mintuna uku ya fice cikin ɓadda kama ya nufi sashen Miran Jasim. (Miran Jasim ɗane a wajen Ameera Banafsha, matar Tajwar Abdul-majeed ta biyu, shine ɗa na huɗu a wajensa, a maza kuma na biyu. Miran Arshaan ke bi masa. Sam babu jituwa tsakanin Ameera Banafsha da Malikat Haseena, ko mutuwar Miran Nayyar an dangantata da Ameera Banafsha a wancan lokacin. Sai dai da yake yaƙin sunkuru ne tsakanin matan biyu duniya bata san da haka ba. Burin Miran Jasim shine mulkar kujerar Shahan-shan tun yana ƙarami kamar yanda mahaifiyarsa ta horesa a kai, dan haka tayi matuƙar gwabza ɓoyayyen yaƙi akan marigayi Tajwar Haysam akan haihuwa har ALLAH ya bashi Tajwar Eshaan. Haihuwar Tajwar Eshaan wata ɗimuwace a nasararsu, saboda haka sun aikata abubuwa da yawan gaske na ganin bai kai ga matsayin da yake a yanzu ba ciki harda karkato da hankalin Miran Arshaan babban ɗa ga Ameera Aasfah amintacciya a wajen Malikat Haseena miji kuma ga Jasrah. Miran Arshaan sam bai biyo ƙyawawan halayen mahaifiyarsa ba, munafuki ne shima kuma yanada boyayyan nasa sirrin duk da riƙo irin na uwa da Malikat Haseena tai masa bayan rasuwar mahaifiyarsa, shiyyasa ya yarda ya haɗa kai da Miran Jasim domin kauda Tajwar Eshaan. Amma kaico UBANGIJI shi mai bawa wanda yaso ne, dan gashi dai Tajwar Eshaan ya zama Shahan-shan a daular ruman. Amma hakan baisa sun bar ƙulla-ƙulla na ganin cikar burinsu ba. ALLAH yasa kun gane🥲). Miran Jasim da dama tsumayen isowar Miran Arshaan ɗin yake ya miƙe daga zaman ƙasaitar da yay a katafaren falonsa da ya jiku da kayan more rayuwa. Juna suka tsirama ido cikin nazari dan bayan ƙullin tsakaninsu kowa nada ɓoyayyen sirri na akan ɗan uwansa. Miran Jasim ne ya fara kauda kansa ya maida hannayensa baya ya goya ya tako a sannu har tsakkiyar falon. Hakan yasa shima Miran Arshaan ɗin ƙarasa shiga suka tsaya gab da juna. “Arshaan Akh Barka da isowa”. Kai Miran Arshaan ya jinjina masa, sai kuma shima ya maida hannayensa ya goya a bayansa tare da ɗan takawa ya koma ta gefensa yana fiskantar window. Murmushi Miran Jasim yayi tare da juyowa yana kallonsa. Shima ya ɗan taka ya sake komawa gabansa. “Arshaan Akh kayi shiru, bayan kuma naga magana mai muhimmanci a cikin idanunka kamar yanda ka sanar dani ta waya”. Huci Miran Arshaan ya furzar, sai kuma ya ɗago suna kallon juna shi da Miran Jasim ɗin. “Jasim Akh akwai damuwa ne. Yanzu nakeji wajen Zawjata. A ziyarar Yaron can ta yau wajen kakarsa akwai shirya ganawa tsakaninsa da yarinyar da shashashar matar can da ban san amfaninta garemu ba tasa muka aura masa”. “What! Waye yay wannan ƙullin?”. “Bana tunanin kana buƙatar tambaya dan kasan wace gadararriyar ce zata iya yanke wannan hukuncin. Na gaji da ganin matar can a raye.” Murmushi Miran Jasim yayi da cije lips. Cikin ɗacin murya ya ce, “Ba Bushirat bace ta cancanci mutuwa. Waccan tsohuwar ce Arshaan Akh. Sai dai kuma su duka bazasu mutu yanzu ba”. “To sai yaushe?”. “Sai sunyi kuka akan gawar wancan shashashan yaron kamar yanda sukai kuka akan ta ubansa”. Karan farko Miran Arshaan ya saki murmushi. Sai kuma ya warware hanunsa da ɗage kafaɗa. “Hakan ma shiri ne mai ƙayatarwa. Yaya batun uban yarinyar da ɗan uwanta? Dan sun sami Barrister Abdullah Aas a yanzu haka”. Da sauri Miran Jasim ya kallesa. “Miyasa ban san wannan ba?”. “Saboda bashi da muhimmanci dan na gama musu talala”. “Arshaan kasan kuwa wanene Barrister Aas?”. “Duk yanda saninsa zai iya bani tsoro ai bai kai razanin sanin muɗin su wanene ba a garesa nake ji?”. “Ba ina maka magana bane akan ƙarfin iko”. “Mi kake son na sani?”. “Ba lokacin sanin tarihi bane. Kawai kayi duk yanda zakai na ganin ya dakata, su kuma a canja musu wajen zama”. “Wai miyasa muke bukatarsu a raye?”. “Saboda sune makamin da zamu juya yarinyar a ƙarƙashin ikon mu yanda muke so”. “Kenan bamu da buƙatar matar hadimin can itama, dan ta gama mana aikinmu”. “Matsalarta mai sauƙi ce. Daƙile Barrister Abdallah Aas ce mafi muhimmanci daga daren yau zuwa yinin gobe. Sai dai ina son a masa talala ta hanyar sanin inda suke kafin ya tsinta kansa a ramin damisa in har baiji gargaɗin farko ba”. Miran Arshaan ya lumshe idanu da sakin siririyar dariya idonsa akan Miran Jasim. Shima dariyar yayi da masa jinjina....... ★... ★★.... ★.... A sashen Malikat Haseenah ma an gama shirya komai na tarbarsa, tun daga kan abincin da yake ci tare da kakar tasa har zuwa tsaftar sashen ma a yau ta kasance ta musamman duk da a kullum a tsaftace yake. An shirya kalolin abinci da ƙamshinsu tun duhun magrib ya cika ko'ina na sashen har maƙwafta ma na iya jiyowa. Abincine da Daneen Ammara ta girka sa da kanta saboda kar a cutar da shi ta hanyar girkawar, sai taimakon ƙanwar Malikat Haseenah da suke kira Yumma. Gab da ƙofar fadar Malikat Haseena lafiyayyar motar da yake ciki ta tsaya, cikin rawar jiki ɗaya daga cikin Hadiman ya buɗe masa, sauran kuwa tuni sun zube ƙasa kan gwiyawunsu kawunansu a ƙasa domin girmamawa a garesa. Yaja fin mintuna biyu bai fito ba duk da an buɗe masa, sai da ya mula dan kansa sannan ya ziro ƙafarsa fara tas dake a cikin ƙyaƙyƙyawan blue ɗin takalmi mai tsananin taushi da ɗaukar ido da zai iya birge duk wani mai kallo, half cover irin na masu sarauta, kusan sakan biyar a tsakani sannan ya ƙara zuro ɗayar cike da ƙasaita. Tashin ƙamshin turarensa da takun sawayensa ya tabbatar ma Malikat Haseenah isowarsa. Da hannu taima dukkan amintattun hadimanta dake zagaye da ita nunin su fice. Har rige-rigen bin ƙofar da zata kaisu falon farko dazai fiddasu ta ainahin ƙofar sashen nata suke. A nutse tsohuwar ta ɗago idanunta ta sauke a ƙofar dai-dai shigowarsa. Tar-tar yake kallonta a cikin hasken ƙwan lantarkin daya haske falon kamar yanda itama take kallon ƙyakyawar fuskarsa dake a tsuke. Tai murmushi da jan numfashi ta fesar a hankali lokacin da yake isowa gabanta. Farin hannunta da fatar ta gama tattarewa saboda tsufa ya ɗan rissina ya kamo tare da kai tausasan lips ɗinsa ya sumbata. “Amincin ALLAH da yardarsa su tabbata ga managarcin tushe mai cike da tsaftatacciyar yabanya”. Idanunta ta lumshe a hankali da sakin murmushi a lokaci guda, sai kuma ta buɗesu tare da buɗe masa hannayenta. Rungumeta yay shima yana sakin ƙasaitaccen murmushi a karo na farko. Tsahon sakan talatin suna a haka kafin su saki juna ya dago amma bai ɗaga daga ranƙwafen ba. Hannunta ta ɗaura saman tausasashiyar sumarsa da a kallo guda zaka tabbatar da kuɗaɗen da take lashewa bazasu kasance na wasa ba. “Aminci da yardar UBANGIJI ta kasance tare da kai kaima farar yabanya abin alfaharina”. Idanunsa ya ɗan ƙankance da jinjina kansa yana murmushin da ita kawai ke iya ganinsa kai tsaye a fuskarsa kamar haka, sai ko Malikat Bushirat. Daga haka ya miƙe da ƙyau ya zauna ƙasan tattausar dardumar da aka shirya musu abinci, zama yay irin zaman sarakai da suka isa suka tumbatsa. Idanunsa ya zubama kakar tasa da murmushi ya gagara barin fuskarta, dan duk wannan ranar tanajinta rana ta musamman ne a gareta, sakamakon tuna mata da mijinta da ɗanta da takeyi da kuma tsananin ƙaunar jikan nata a yanzu. “Nannah Kina lafiya?”. “A zahiri dai lafiya nake, amma a baɗini cike nake da kewarka da ƙishirwar son ganinka a idaniyata Hafeedi”. “Uhhm!” ya faɗa da ɗan lumshe idanunsa ya buɗe a lokaci guda. “To ki koma sashena mana, in har da gaske ne kina mun irin wannan buƙatar a kusa da ke”. Yay maganar da yanayin zolaya, sai dai fuskar a kame take babu alamar hakan tattare da shi. Itama murmushi tai batare da tace komai ba dai-dai tana miƙa masa kofin data zuba madara. “Kwana biyu mike faruwa da kai?”. Yaja wasu sakanni kafin ya girgiza mata kansa alamar babu komai. Idanu ta cigaba da tsura masa har hakan ya ɗan sakashi tsarguwa ya kauda kansa gefe. Itama ɗauke natan tai gefe cikin rashin bama yanda yay ɗin muhimmanci. Sun kwashe kusan mintuna uku a yanayin shiru kafin shi ya katse hakan. “Mamy fa?”. Yay maganar a fisge tamkar yinta ya zama tilas ne a garesa. Ita ɗin ma a ƙasaitancen ta bashi amsa da “Suna zuwa”. Idanunsa masu girma da haske ya tsira mata. Kanta ta ɗauke gefe dan tasan kalmar (Suna zuwa) ɗin ce yake nemawa amsa.. Shima janye nasa idanun yay cike da basarwa da ƙasaitarsa ya ɗauka kofin data zuba masa madara...... A dai-dai nan Daneen Ammarah ta shigo da sallama hanunta riƙe dana Iffah dake cikin ƙyaƙyƙyawar doguwar rigar abaya baƙa datai matuƙar amsar jikinta, Shirine na musamman da Daneen Ammarah ta zauna domin yinsa gareta da kanta. Cikin ƙanƙanin lokaci sirrintaccen ƙamshin jikinta ya shiga rige-rigen isa hancin Malikat Haseena da mai gayya mai aiki. Shaƙar ƙamshin turaren da zaton Daneen Ammarah ce kawai mai shigowar ya sashi ɗago idanunsa, cikin Sa'a kuwa ya sauke su a kanta. Murmushi Daneen Ammarah da suka haɗa ido ta sakar masa, yayinda shi kuma fuskarsa ke nuna tsananin ƙaunar da yake mata a zahiri. Haka itama Malikat Haseena murmushi ne ƙawace a fuskarta idonta akan Iffah da kanta ke rissine taƙi kallon komai. Ƙara riƙe hanun Iffah Daneen Ammarah tai da ƙyau kamar za'a ƙwace mata suka cigaba da takowa a nutse. Malikat Haseena taima Daneen Ammarah nuni ta zaunar da Iffah a kusa da ita, sai ya zam suna facing juna da Tajwar Eshaan, sannan kuma a tsakkiyar su shi da Malikat Haseena ɗin.. Gaba ɗaya ya tattara hankalinsa ga Daneen Ammarah tamkar baiga tana tare da wata ba, “Amincin ALLAH da rahamarsa su tabbata ga Mamy na!”. Ya faɗa akan laɓɓansa kamar bashi yay maganar ba, dan ko Iffah da Malikat Haseena ba jinsa sukai ba sai ita Daneen Ammarah da takai zaune kusa da shi. itama ta sake sakin murmushi da kaɗa masa kanta. “Tare da kai Abni, Amincin ALLAH da rahama da kariyarsa su tabbata a gareka. Ina fatan kana cikin ƙoshin lafiya da nutsuwar zuciya?”. Kansa kawai ya kaɗa mata, sai kuma ya ɗan ɓata fuska. Murmushi ta sake saki da maida idanunta kan Iffah da Malikat Haseena kema magana. “Hafed-ti! An hanaki barci ko?”. A hankali Iffah da ƙirjinta ke faman harbawa da sauri-sauri ta girgizama Malikat Haseena da tai maganar kanta. Cikin sanyin murya da sauƙaƙa fitar sautinta ta ce, “A'a Mamma ai bamma kwanta ba”. “Masha ALLAH yaya jikin naki?”. “Alhamdulillahi Mamma, Aminci ALLAH ya tabbata a gareki a wannan lokaci”. “Amin. tare dake kema Negar”. Iffah ta ɗan murmusa har yanzu kanta a rissine. Daneen Ammarah dake kallonsu da murmushi ta janye idanunta ta maida ga Shahan-shan daya sake ɗauke kansa tamkar bai san mike faruwa ba ma. “Ibnati!”. Ta kira sunan Iffah a tausashe kamar yanda ta saba. “Na'am Mamy”. Itama ta amsa mata kamar yanda ta saba. Sai dai ta kasa iya ɗago kanta, dan duk da bata san wanene ba gaba ɗaya kwarjininsa ya cika falon har tanajinta a matuƙar matse kamar ta tsilla da gudu kozata samu nutsuwa.... “Ga yaro na”. Ta faɗa cikin sigar son ɓiye mata ainahin wanene ɗin. Iffah da bata damu da son sanin gaskiyar zancen Daneen Ammarah ɗin ba ta amsa da alamar raunin murya a tare da ita. “Amincin ALLAH ya tabbata a gareka. Barka da wannan lokaci”. Shiru babu alamar zai amsa mata, ran Iffah ya sosu dan a rayuwa ta mugun tsanar wulaƙanci, duk yanda taso ta danne sai ta kasa, a karan farko tun shigowarsu falon ta ɗago idanu cike da jin zafi, dai-dai ya ɗan ɗago shima zai kai kofin madara bakinsa idanunsu suka rufta cikin na juna... Zabura Iffah tayi da ware manyan idanunta, yayinda shima yay ɗan tsai yana kallonta na sakanin da basu gaza biyar ba, sai kuma ya janye abinsa cikin halin ko'in kula ko fahimtar yanayin data shiga ya sake gyara zaman ƙasaitarsa.......✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_26_* ........“Ya rabbi. Aljanin can dai”. Harshen Iffah da zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri ya suɓuce wajen faɗa batare data shirya hakan ba..Malikat Haseena da furucin Iffah ya shiga kunnuwansu a bazata duk suka ɗago suka kalleta. “Ibnati! Aljani kuma a ina?”. Cewar Daneen Ammarah a mamakance”. Yawu Iffah ta haɗiya da ƙyar, sai kuma ta girgiza kanta da sauri tana ƙaƙaro murmushi. “M... M.. Mamy bance komai ba”. Tai ƙoƙarin kare kanta da rawar harshe. Magana Daneen Ammarah tai ƙoƙarin sake yi Malikat Haseena ta ƙyafta mata idanu. Dole ta haɗiye ta maye gurbinta da murmushin son basarwa. Jikin Iffah tsuma yake, amma tanata ƙoƙarin son hana fitowar hakan ta hanyar matse kanta waje guda da ambaton sunayen ALLAH a jajjere ko zata farka a ruɗanin da takema kallon gizo ko tabbacin abinda take tsoro wato Aljanin can ya cigaba da bibiyarta. Daneen Ammarah na ƙoƙarin haɗama Tajwar Eshaan abinci Malikat Haseena ta girgiza mata kai da yi mata nuni da Iffah ta wutsiya ido. Amsa mata tai cikin lumshe idanu da buɗesu akan Iffah. “Ibnati”. A ɗan zabure Iffah ta ɗago ta dubeta. Itama da idanu tai mata nuni da abincin. Sam Iffah ba fahimtar Yaren nan nasu ta cika yi ba kai tsaye, dan haka tai ɗan tsamm tana kallon Daneen Ammarah ɗin har sai da ta furta mata da baki. Numfashi ta sauke a hankali bana samun nutsuwa ba, na sake shiga ɗimuwa da kaikawon bugun zuciya, a saɓule ta motsa ta miƙe dan tayi ɗan nisa da shi, ta bayan Malikat Haseena ta zagaya ta koma kusa da shi ta durƙusa. Ta gefen ido ta ɗan sake kallonsa cike da taraddadi, cikin sauri ta kauda idanun dan abinda ta gani ɗazun ne dai ta sake gani, ta jawo numfashin dake neman kufce ma ƙirjinta da ƙyar.... “Ki haɗa masa waɗan nan”. Daneen Ammarah ta katseta ta hanyar nuna mata abinda ke cikin kwanikan gabansa.. Da ƙyar ta iya amsa mata da to, sannan ta kame jikinta dake rawa, ta ɗan duƙo zata ɗauka abu ƙamshin turaren da bazai taɓa ɓace mata ba ya daki hancinta, da alama wanda take shaƙar ne tun ɗazun ya dannesa saboda ba'ayi amfani da shi ba a yanzu ko kuma wani abu da ban. Da sauri ta ɗan ja jikinta baya jininta na tsinkewa, yanzu kam duk yanda taso dannewa sai da halin da take ciki yaso bayyana.... “Hafed-ti! Ko jikin ne?”. Malikat Haseena ta jeho mata tambayar da har shi kansa sai da ya ɗan kallesu ta gefen ido. Kanta ta girgiza mata tana ƙoƙarin danne abinda ke neman fin ƙarfinta na ruɗani. “Ina cikin godiyar ALLAH Mamma”. Murmushi Malikat ɗin tayi cikin cigaba da nazartar ta harta kammala. Sosai kanta ke juya mata, dan haka ta koma mazauninta da jan jiki tamkar ta tsala ihu ko hakan zai bayyanama kowa a wane hali take ne... Ko sau ɗaya Iffah ta kasa kai abincin bakinta, sai faman juya spoon take da satar kallon yanda yake tsakurar nasa abincin shima cike da ƙasaita. Lura da bata ci yasa Daneen Ammarah mata magana. Sai kawai tai murmushi da ɗan ɗiba kaɗan takai bakinta, juyashi take a hankali kamar mai tauna magani, dai-dai shi kuma ya ajiye nasa cokalin zai ciri tissue suka haɗa ido a karo na biyu. Da ƙarfin zuciya taso janye nata amma yaƙi bata damar hakan, sai ma jan nashi da yay cike da salo kamar zai lumshe ya sake buɗe su a tsakkiyar ƙwayar nata. Ƙwarewa tai tsabar lamarin yazo mata a bazata.. Daneen Ammarah da Malikat Haseena suka zabura kanta baki ɗaya, da kyar ta iya buɗe baki ta amshi ruwan da Malikat ta saka mata a baki, yayinda Daneen Ammarah ke faman shafa bayanta tana jera mata sannu.. A dukkan bidirin da ake idan dutse ya motsa Tajwar Eshaan ya motsa. Har tarin ma ya lafama Iffah ta samu daidaiton numfashi. Koda ganganci bata sake yunƙurin duban sashen da yake ba har lokacin tafiyarsa yay, duk yanda taso zamewa a masa rakkiya da taga Daneen Ammarah da Malikat Haseena na shirin yi hakan bai yiwu ba, dole ta bisu har waje. Tana ta faman ɗauke kanta amma tamkar wani sihiri sai da suka haɗa ido dai-dai zai shiga motar da aka buɗe masa. Wani irin karsashi da ƙwarin gwiwarta ne a bazata suka dawo jikinta, ta yamutse fuska da tsuke baki ta fincike nata.. Yayinda shi kuma ya ɗan motsa bakinsa tamkar mai son yin murmushi ko magana.... (🤔???) ★★..... Ruɗani, mamaki, al'ajabi sun taru sun hana Iffah runtsawa a wannan dare. Kanta ya gama kullewa dangane da abinda duk suka faru ɗazun. Shin mutumin nan aljanin ne da gaske? Kokuwa wani abu daban da bata sani ba. Babu abinda ke mata kaikawo a zuciya sai haɗuwarsu ta baya har sau uku, kenan idan lissafin ta yayi dai-dai shiɗin jikan gidan nan ne tunda Daneen Ammarah ta kirasa da ɗanta, kamar yanda Malikat Haseena ta kirasa da jikanta. Shiyyasa yake komai cike da ƙasaita da izzar da ko Shahan-shan ɗin da kansa iyakar wadda zaiyi kenan ai. Ita kam al'amarin wannan gida ya fara birkita mata lissafi. A lissafin ta dai Daneen Ammarah aka haifa a gidan nan, Hakan na nufin ta rabu da mahaifinsa ne? Kokuwa a cikin gidan itama take auren? Dan ita dai tunda tazo anan take ganinta babu alamar tana da wani miji ko gidan zama bayan nan ɗin.. “Ya rabbi” ta faɗa a fili tana mai jan nannauyan numfashi ta fesar..... *_WASHE GARI_* A ɓangaren Malikat Haseena ma yanda Iffan ta kusan raba dare tana juya al'amura a ranta haka itama ta raba dare wasiwasi akan abinda ta fahimta da wanda ta nazarta. Data kasa cigaba da riƙe abinda ke mata kaikawo tana idar da sallar asubahi ta bukaci ganin Daneen Ammarah. A ɗan rikice ta shigo da tunanin ko ta kwana babu lafiya ne. Ganinta zaune sumul ya sata sauke ajiyar zuciya takai zaune kusa da ita. “Wlhy Mamma hankalina har ya tashi, nayi zaton ko kin kwana babu lafiya ne”. Ɗan murmushi tai batare datace mata komai ba. Sai dai ta miƙa mata maganin da ake shafa mata a kafafu. Amsa tai babu musu ta fara shafa mata itama tana murmushin. “Ammarah mi kika fahimta?”. Ta jeho tambayar tata kai tsaye ga Daneen Ammarah. Cikin rashin fahimta Daneen Ammarah ta ɗago. “Mamma akan mi?”. “Haɗuwar Malik da Zawjata-almilk”. “Mammah har kin sakani dariya, Miya kawo wannan maganar kuma?”. “Ke dai amsa mini ita”. “Ban san mi kike son sani ba Mammah, amma nidai nasararmu da dacewarsu matsayin ma'aurata na hanga tattare da su”. Murmushi Malikat Haseena ta saki da kauda kanta. “Ni kuma ba hakan kawai na hanga ba”. Idanu Daneen Ammarah ta tsura mata batare da tace komai ba. Malikat Haseena datai shiru itama kamar bazata cigaba da cewa wani abu ba ta nisa. “A nazarin danai musu tamkar akwai sanayya tsakaninsu kafin haɗuwar jiya”. “Sanayya kuma Mammah? Idan da na fahimta sun san juna kenan kike nufi?”. “Haka”. “Haba Mammah a ina to zasu san juna? Karki manta Abni ba fita yake ba. Ƙaddara ma yana fita, wanda ke zagaye da tsaro ta ina sani da mu'amula mai ƙarfi irin wadda kike hasashe zasu ƙullu tsakaninsa da yarinya mai matsayinta. Karfa ki manta ko'a cikin gidan nan ba kowa ya san fuskarsa ba balle talakawan dake rayuwa a waje”. “Wannan shine abinda ya ɗaure kaina nima. Sai dai azuciyata na faɗamin akwai abinda yake ba daidai ba da saninmu tabbas”. “Kamar mi kenan Mammah?”. “Nima amsar da nake nema kenan”. Babu wanda ya iya sake cewa komai sukai shiru kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa...... ★★..... ★★.... ★★..... Alhamdullah Barrister yaci nasarar gano inda su Babiy suke, sai dai ba'a jiya ba kamar yanda ya faɗama su kaka har suka zauna zaman jira sai da sukaga yamma tayi babu wani bayani sannan suka haƙura suka wuce. Bai ɓata lokaci ba kuwa yay kiran Abu Zainab ya sanar masa. Shima cike da zumuɗi ya nufi gidan Babiy domin sanar ma Kaka. Sai dai kuma ya tarar yaje masallaci kasancewar lokacin sallar zuhur yayi. Dole ya shanye zumuɗin nasa shima ya tafi masallacin. Bayan an idar da salla ƙofar masallaci ya fito ya tsaya yana kallon duk mai fitowa. Daga can ciki kuwa Kaka dake a cikin mutanen da suke sahun farko sai a karshe suka sami damar miƙewa suma. Ya ɗaga zai miƙe mutumin dake a kusa da shi ya bashi hannu alamar suyi musabaha. Babu musu ya miƙa masa nasa yana ɗan murmushi. Mutumin da shima murmushin yake ya tsaida kwayoyin idanunsa a tsakkiyar na kaka, hakan yasa shima Kaka cigaba da kallonsa dan ya fahimci akwai wani abu.... “Nasan kasan girman alkairi tsoho. To karka yarda ka maida shi da sharri ga wanda yay maka. Dan haka ina baka shawarar hana waɗan can mutanen biyu cigaba da shiga abinda bai shafesu ba. Inba hakaba kuwa kai da su kuna gab da zuwa inda surukinka da jikanka suke yanzu. Na Barka lafiya”. Mutumin ya kare maganar da zare hanunsa a cikin na Kaka ya miƙe. Da kallo kawai kaka ya bisa harya ɓacema ganinsa. Kafin yaja numfashi ya fesar tare da miƙewa zuciyarsa na faman kaikawo tamkar zata fito. Koda ya fito da Abu Zainab ya fara cin karo, ya tsira masa ido na wasu sakanni kafin ya karasa garesa. Abu Zainab da shima ya hangosa cike da zumuɗi ya tarbesa, ko gaisawa basuyi ba ya rankwafa dai-dai kunnen kaka ya gwargwaɗa masa saƙon Barrister... Murmushi kaka ya saki na ƙarfin hali, sai kuma ya jinjina kansa da ambaton Alhamdullah a hankali. Abu Zainab da bai gama fahimtar yanayin kakan ba cike da zumuɗi yace, “Baba muje Barrister na jiranmu yanzu haka”. Idanu kaka ya tsira masa tamkar zai ce a'a. zuciyarsa na tuna masa girman alkairinsu garesa, tabbas bazai so saka rayuwarsu a gariri su da iyalansu ba, idan ma yaga wani zai zama sanadi zai bada karfinsa wajen karesu. Kalaman wancan mutumin sun sake tabbatar masa akwai lauje cikin naɗi game da kama su Babiy, hakama ƙin amsar Ummu a asibiti waccan ranar. Hakan na nufin kuma duk kaikawon da suke ana biye da su....... “Baba kaga gashi ma yana kirana”. Abu Zainab ya katse masa tunani. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke, yanda Abu Zainab ya ƙagu ya sashi fahimtar bashi da isasshen lokacin tunani, zai bari sai ya samu nutsuwa ya bi hanyar data dace badan masu kurarin sunfi ƙarfinsa ba. Sai dan kawai baya son bin wata hanya daya jima da kyamatarta a ransa, amma da su ko inda yake basu isa tunkara ba balle jininsa..... *_BARRISTER_* Barrister Abdallah Aas ya ajiye wayar daya janye manne a kunensa alamar waya ya gama. Kallonsa ya maida ga sakatarensa dake ƙoƙarin ficewa saboda ganin yana waya. “Suhail”. Ya dakatar da shi ta hanyar kiran sunansa. Amsawa yay tare da juyowa cikin girmamawa. “Akwai damuwa ne?”. “A'a Sir. Wani mutum ne dai ke buƙatar ganinka. Nayi ƙoƙarin fahimtar da shi kanada uziri amma bai saurareni ba”. Ɗan jimm yay kamar mai nazari, sai kuma ya huro iska da kaɗa kai. “Okay ba damuwa shigo da shi kawai na gansa kona minti goma ne dan zan fita ne”. “Okay Sir”. A yanayin da mutumin ya shigo ya saka Barrister tsira masa ido, yakai zaune tun kan a bashi izini yana cigaba da bin office ɗin da kallo tamkar mai irge kayan cikinsa. Sai kuma ya juya ga Barrister tamkar wanda aka bama umarni ya miƙa masa hannu. Kamar Barrister zai noƙe sai kuma ya miƙa masa shima. “Am sorry Barrister nasan baka Sanni ba. Na kuma shigo kai tsaye batare da neman damarka ba” ya saki murmushi da cigaba da maganarsa batare da ya bama Barrister ɗin damar cewa wani abu ba. “Kar sani na ya zama damuwar abinda ya kamata ka sani dangane da ni, mafi muhimmanci kawai kasan miya kawo ni”. Ya kai ƙarshen maganar da ɗakko jakkar daya shigo da ita ya ajiye saman tebirin Barrister. “Waɗan nan kuɗaɗene da zasu isheka tsahon wani lokaci kana amfana, ina son ka manta da zancen aikin da surikinka ya kawo maka, idan son samu ne ma daga yau ka dakatar da shi shiga abinda bai shafesa ba”. “Duk akan wane dalili zanyi hakan?” Barrister da ɓacin ransa ke yunkurowa ya faɗa cikin son dannewa. “Ba dalilin ya kamata ka sani ba. Ƙin bin shawarar ne matsalarka Barrister”. Cikin bayyanar fushin Barrister gaba ɗaya akan fuska ya yunkuro zaiyi magana ring ɗin wayarsa ya dakatar da shi hakan. Atare suka kalli wayar sannan suka kalla juna. Wayar mutumin ya nuna da sakin murmushi, “Bismillah”. Barrister yaja ƙaramin tsaki da hararsa tare da kai hannu akan wayar dake cigaba da ɓurari.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 90165991 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_27_* .......“Assalamu alaikum”. Ya faɗa a daƙile saboda rashin sanin wanene. A maimakon amsa masa sallamarsa aka ambaci sunansa tamkar a lokacin ake raɗa masa shi. “Barrister Abdallah Ibn Adam Aas! Kar kayi taurin kai, dan zaka iya rasa kanka dama waɗan da kake yunƙurin taimakawar. Ni umarni nake baka ba shawara ba kamar shi, domin hatta iyalanka ba zasu tsira ba daga tarko na”.. Ɗan zabura Barrister yay tamkar wanda cinnaka ya ciza. Daga can aka cigaba da magana cike da isa. “Suna hanyar zuwa gareka, ya rage naka tun yanzu ka raba gari da su, ka kuma gargaɗi surikinka. Na barka lafiya”. Yana kokarin yin magana ƙitt aka yanke kiran. Ciro wayar yay da sauri daga kunensa, ganin ta yanke yay ƙoƙarin kiran number... Mutumin dake tare da shi ya miƙe yana dariya. “Barrister shawara karma ka wahal da kanka dan basake samunsa zakai ba har abada in har a wannan layin ne. Na barka lafiya”. Da ƙyar Barrister ya kwato numfashinsa gab da mutumin zai fice. Cikin jarumtarsa ya dakatar da shi a ɗan tsawace. “Ni kurari ko gizago basa firgitani ai. Dawowa ka ɗauka trash bag ɗinka zai fi maka alkairi fiye daka barta anan ta zamewa rayuwarka BAYA DA ƘURA. wannan shawara ce”. Har cikin rai maganganun Barrister sun sokesa. Amma kasancewar sa ɗan hannu a iya bariki sai ya saki murmushi. Batare da yace komai ba yay salute ɗin Barrister dake masa kallon ƙasƙanci yay ficewarsa. Baya Kaka da Abu Zainab dake yunƙurin shigowa office ɗin suka ja dan kaɗan ya rage suyi gware. Suna masa sallama bai ko amsa su ba yay musu kallon ƙasa da sama yay wucewarsa. Basu damu ba, dan daga ganinsa kaga babban mutum. Barrister da aka bari da juyawar kai ya amsa musu sallama cike da son danne ɓacin ran dake a fuskarsa. Sun gaisa da mutuntawa kamar yanda suka saba. Fuskar Kaka da ɗan murmushi ya ce, “Ashe kuma an dace da sanin inda suke?”. Murmushin ƙarfin hali Barrister yayi da jinjina kansa, ya jawo wani file dake gefensa. “Nima banyi tunanin abin zai zo mana da sauƙi haka ba Baba. Amma Alhamdullah addu'a bata faɗuwa ƙasa banza. Inaga muyi azamar zuwa ma kar'a samu wani tazgaro kuma kasan halin ƙasar tamu”. Daga Kaka har Abu Zainab sunyi na'am da hakan. Duk suka miƙe babu ɓata lokaci suka fice kowa da abinda ke masa kai kawo a cikin rai musamman Kaka da Barrister..... *_MASARAUTA. (MALIKAT BUSHIRAT_* Cikin zumuɗin son jin yaya haɗuwar Shahan-shan da Zawjata-almilk ta kasance a jiya Malikat Bushirat tai shirin ziyartar sashen Malikat Haseena a yau. A ƴan rakkiyarta har da Jasrah dake son sake duba jikin Iffah. Tuni ƴan leƙen asirin cikin hadimai sun kwasa zuwa sassan iyayen gijinsu kuwa. Dan wannan ya zama kamar al'ada a masarautar kowane ɗan leƙen asiri kan kai wa uwargijiyarsa ko uban gidansa duk wani motsin wani babba a daular. Ta wannan hanyar ne a mafi yawan lokuta abubuwa ke yaɗuwa kunnen duk wani mai faɗa aji na gidan musamman abinda ya kasance na sirri. Malikat Bushirat ta samu tarba ta girmamawa ga surukar tasu a fadarta. Tuni hadimai sun cika gabansu da kayan motsa baki. Kasancewar ganawar ta shafi wani yanki na ɓoyayyen sirrinsu duk wani hadimi aka sallamesa. Katafaren falon ya kasance daga Malikat Haseena sai Malikat Bushirat da Jasrah sai Daneen Ammarah. Tattaunawar ta jasu tsahon lokaci kafin Malikat Haseena ta aika amintacciyar hadimarta Banou kiran Iffah.... ★Sam Iffah dake cikin wani yanayi na tsananin faɗuwar gaba da sanyin gaɓɓai sakamakon mummunan mafarkin da tai akan su Babiy a barcin zuhur daya figeta bata san mi ake ba saboda bata fita ko'inaba yau iyakarta ɗakinta. Yanzu hakama da aka idar da sallar la'asar tana tsumayen Daneen Ammarah ne kamar yanda ta saba, dan duk yinin yau ma basu haɗu ba tun bayan idar da sallar asuba dai data fita ta gaishesu kamar yanda ta saba ita da Malikat Haseena. Hadimai dai sun kawo abinci tare da saƙon gaisuwa daga Daneen Ammarah ɗin ɗazun da rana akan cewar tana nan tafe. Malikat Haseenah ma kullum da kanta takan zo ta duba ta, kasancewarta tsohuwa mai dattako da iya zama da mutane tuni ta shige zuciyar Iffah itama, dan duk da bata da sakewa da yawan fara'a har dan jan Iffah take da hira. Sallayar datai sallar ta linke har yanzu jikinta a sanyaye ga damuwa fal ranta akan iyayenta, acan ƙasan zuciyarta takeji akwai wani mummunan abu dake sake tunkarota koma ya riga ya iso garetan ta hanyar iyayenta batare data sani ba. Yanayin ɗan zafi da ake ya sata yaye mayafin abayan data naɗe kanta da shi ta ajiye, ɗaurarren dogon baƙin gashinta dake reto a tsakkiya ya bayyana. Abincin da aka shirya mata tun ɗazun da bata ci ba ta nufa, ta bubbuɗe taga komai, batama jin cin komai har yanzun, dan haka ta tsiyayyi madara kawai da shanta tamkar al'adar ƴan ƙasar ne. Tana buƙatar fara canja kayanta zuwa marasa nauyi, dan haka ta ajiye kofin madarar a bedside drawer. Toilet ta fara shiga ta fito sannan ta shirya cikin wata yar yololuwar rigar mara nauyi mai zubin shimi. Iyakar rigar gwiwar ta ne, gata kalar fari da adon jajayen firanni. Ta matuƙar haskata da fidda ƙuruciyarta tamkar ƴar budurwar balarabiya. Turarrukan da Daneen Ammarah ta tule mata ta zaɓa kusan kala uku ta fesama jikinta. Cikin nutsatstsen takunta ta dawo saman gadon tana mai kallon fatar hanunta dake jajir saboda saɓar da tayi. “ALLAH dai ya isana wlhy” ta faɗa cike da halin tsiwarta tana jan bargo ta rufa iya cinyoyinta bayan ta jingina jikinta da fuskar gadon. Littafin da take rubuce-rubucenta na duk abinda ya faru ta ɗauka ta buɗe ko zata ji sassaucin tunane-tunen da zuciyarta ke mata marasa daɗi akan iyayenta, dan sam mafarkin nan yaƙi barin ranta koda na sakan ɗaya... A zahiri rubutun tai shirin fawara, dan yanda ta tsurama littafin ido da riƙe biron da nutsuwa matuƙa zai saka ka hasashen haka. Sai dai sam ko kalma biyu ta kasa rubutawa tamkar ma an mata wankin ƙwaƙwalwa komai ya gudu, hasalima nisan da tai a tunani yasa bibbiyu take ganin rubutun baya da tayi.... Knoking ƙofar da akai ya sata jan numfashi ta fesar, sai kuma taja mayafin dake gefenta ta yane jikinta har saman kanta tare da amsawa da “Yes! Kowaye ya shigo”. A ɗarare hadima banou ta shigo, tsananin tsoron Iffah shimfiɗe akan fuskarta ya kasa boyuwa. Daga bakin ƙofar ta zube muryarta na ɗan rawa kamar yanda jikinta ke tsuma. “Amincin ALLAH da lafiya su tabbata ga Zawjata-almilk”. Harara Iffah dake kallonta ta zabga mata. “Ina tare da masu lashe kurwar mutane irinku lafiyar zata tabbata a gareni? mtsoww!! Malama faɗi abinda ya kawoki bana son gulma”. Ƙasa Banou ta sakeyi da kanta muryarta na rawa, dan harga ALLAH tana shakkar wannan yarinya da ko magana gatsau take yinta babu alamar shakku tattare da ita. “Uhm uhm dama Malikat ce take buƙatar ganinki”. Hannu kawai Iffah ta ɗaga mata, dan har cikin rai ta tsani matar nan matuka. Sai da ta miƙe zata buɗe ƙofa sannan tai magana a gadarance. “Ki jirani a ƙofa, saura kuma kafin na fito ki lashe mun hadimai azzalumar bamza”. Da rawar jiki data harshe Banou tace, “Hakan bazata faru ba ranki ya daɗe”. “Uhm munafuka kamar gaske”. Iffah ta faɗa tana sauka a gadon cikin mita...... ★Tunda suka shigo ko sau ɗaya Iffah bata iya ɗaga kai ta kalla ko ɗaya a cikinsu ba. Saɓanin su da duk suka zuba mata ido cike da jin ƙaunarta a rayukansu. Cike da nutsuwarta ta karasa garesu, maimakon kujera da duk suke zaune sai ta kai ƙasan lallausan dardumar... “Haba Ibnati tashi ki hau sama mana”. Jasrah tai yunƙurin dakatar da ita. Kai Iffah ta girgiza da ɗan murmushi a fuskarta, “A'a nanma ya isa”. Cike da sha'awa da jin daɗi duk suke dubanta. Ta juya ta gaishe da Malikat Haseena, da fara'a da kulawa ta amsa mata tana mai sanya mata albarka. Cikin jin daɗi ta juya gasu Malikat Bushirat ta gaidasu suma. Suma da kulawar suka amsa mata, dan duk ƙasaita da jin kan Malikat Bushirat sai ta tsinci kanta da murmushi da sauƙaƙawa akan yarinyar saboda kwarjini da tai mata. Shiru na wasu ƴan sakkani ya biyo baya, kafin Daneen Ammarah ta katse shirun ta hanyar kiran sunan Iffah. Ta amsa mata da girmamawa sai dai bata iya ta ɗago kanta ba. Daneen Ammarah ta sake kiran sunanta da faɗin, “Kinga ɗago ki kallemu”. Da ƙyar ta iya dauriyar bin umarninta. Dan duk rashin jin Iffah tana da wani hali na girmama duk mai nuna mata ƙauna koda bai cancanta ga sauran mutane ba. “Ibnati nasan nan zuwa yanzu duk kin sammu ko?”. “Eh Mamy”. “Amma baki san matsayinmu ba?”. Nanma tace “Eh Mamy”. “To Alhamdullah yau duk zaki sani. Ina son ki bani dukkan hankalinki nan ki kuma saurare ni yanda ya kamata”. Ta jin jina mata kai. “Kamar yanda nasan kikaji Mamma a garemu mahaifiya ce, itace ta haifi Hama (Suruki) ɗin ki, da ni dama wasu biyu da zaki sani anan gaba sai dai ɗaya ya rasu”. “ALLAH ya gafarta masa”. Ta faɗa cike da rauni. A tare suka amsa mata da Amin. Daneen Ammarah ta ciga da faɗin, “Wannan da kike jin ana kira Malikat Bushirat itace Hamah (Suruka) ɗinki data haifi Shahan-shan na yanzu kuma mijinki da yazo nan jiya......” A razane Iffan ta waro idanu ƙirjinta na wani irin harbawa kamar zai wantsalo. Cikin subutar baki ta ce, “Shahan-shan! Na jiy.....” sai kuma tai shiru ta haɗiye sauran maganar saboda tuna a inda take... “Kin sanshi ne kafin jiya?”. Malikat Haseena dake nazartarta ta jeho mata tambayar a bazata. Da sauri Iffah da zufa ta jiƙema dukkan jiki, ta girgiza kanta. Kasancewar ta gwanar wayo tai saurin faɗin, “Mamma ina mamaki ne dai, ban zaci ganin Shahan-shan ɗin nada sauƙi kamar haka ba”. Kusan a tare suka saki murmushi saboda hango tsantsar ƙuruciya a maganar tata. Sai dai malikat Haseena tsaf ta gama karantar Iffah waskewa tai. Amma kasancewar ta tsohuwa mai dattako sai ta dake itama ta shiga jerin ƴan murmushin.. Daneen Ammarah ta cigaba da faɗin, “Wannan ƙanwa ce ga Malikat Bushirat, Khaalah (Aunt) ga mijinki. Na baki ne a dunƙule iyamu da muke anan saboda muhimmancin abinda zakiji a yanzu”. Kai Iffah ta jinjina mata da alamun gamsuwa. Jasrah ta cigaba daga inda Daneen Ammarah ta tsaya. “Ibnati dalilin miki wannan dogon sharhin a kammu shine fara aikinki matsayin Zawjata-almilk a wannan masarauta. Alhamdullah tunda kinji sauƙi zaki koma sashenki kamar sauran Zawjata-almilk guda biyu, sai dai zaki samu horo daga wasu amintattunmu matsayinki na Zawjata-almilk. Mun zaɓeki ne saboda nutsuwarki da tarbiyyarki. Basai mun zaman sharhi akan abinda ya faru ba a baya kasancewar kema ƴar kasa ce kin san komai na dangane da mutuwar matan Shahan-shan da suka gabata.” Iffah ta haɗiye kududun baƙin cikin daya tokare mata maƙoshi akan famin rasa ƴan uwanta da tai da ƙyar ta jinjina kanta. Malikat Bushirat ta amshe da cigaba da faɗin, “Ibnati kece zaki zama mutum ta farko a rayuwa da zan nema alfarma a gareta, hakan kuma ta faru ne saboda jinki da nake a cikin raina da kallon da duk muke miki anan matsayin wani haske da insha ALLAH zai haska mana duhun da muke ciki. Muna son ki shiga jikin Saiful-malik domin binciko mana ainahin minene matsalar, saboda dukkan waɗan can matan da aka rasa daga kaisu turakarsa ne ake samun matsalar. Mun miki alƙawarin baki dukkan kariyar da bazamu bari ki cutu ba....” (Kariyar UBANGIJINA zata kasance tare da Ni). Iffah ta ayyana a zuciyarta. Malikat Haseena ce ta cigaba da faɗin, “Zamu fara ne da matakai da hanyoyin dinga haɗuwarku daga nan zuwa wani lokaci, fatanmu ki zama mai saka ido a dukkan wani motsinsa, a karan kansa, da duk wasu wanda zasu mu'amulancesa har a cikin hadimai. Kiyi takan tsantsan, dan mutum ne shi mai wayo matuƙa, sannan mai wahalar sha'ani da fahimta. Ba'a gane mi yake nufi ko minene a ransa akan fuskarsa, kar ki yarda ki bashi wata damar da zai iya zargi a kanki. Fatanmu dai ki zama jaruma a dukkan al'amuransa dama na kowa dake a wannan masarauta, duk abinda kikaci karo da shi ba dai-dai ba kiyi maza ki sanar da ɗaya daga cikinmu”. Zantukan nasu ya saka zuciyar Iffah dinga tsalle-tsalle a kan dalilai biyu.......✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_28_* ........Na farko ji a ranta UBANGIJI ya amsa mata addu'ar ta akan burin data shigo da shi Daular ruman. Na biyu minene dalilin waɗan nan mutane na buɗe mata cikinsu?. Na ƙarshe da yafi kowanne razani da ban mamaki a ƙwaƙwalwarta dama suma sun san shike aikata kisan kenan? Amma suka zaɓi yin shiru saboda ba ƴaƴansu ake halakawa ba kokuwa suma tsoronsa sukeji? A ɗan ƙaramin tunaninta tanaga zasu iya yin amfani da ƙwanji wajen sanin mi Shahan-shan ɗin ke aikatawa musamman Malikat Haseena da Malikat Bushirat. Amma miyasa suka zaɓi yin amfani da ita? Kodai sun gama gane manufarta ne a kansa.....? “Ibnati!”. Daneen Ammarah ta katseta daga nisan da tai a tunani ta hanyar kiran sunanta da taɓata. Firgigit kuwa ta kawo ajiyar zuciya. “Karki kasance a dogon nazari, manufarmu ta sakaki a wannan sabgar tana da nasaba ne da dalilai biyu. Na farko juriyarki ta bamu ƙwarin gwiwar kallonki a jaruma. Na biyu jinki wata abu mai muhimmanci da muke fatan nasara ta dalilinta kodan tsallake tarkon masu aikata wannan ɓarna da kika tsallake a harin farko da muke jin shine lagon da aka dinga ɗanawa a farko wajen salwantar da rayukan da suka gabata....” “Mamy nima zata yuwu bana tsallake bane dan nafi ƙarfinsu, maybe na tsallake ne saboda tsayawarku da fatanku akan ganin na tsallake ɗin. Amma tabbas zan iya sadaukarwa, zan kuma iya bin umarninku badan inajin ƙarfina ya kai ba sai dan kun isa ku bani umarni”. Su dukansu kalamanta sunyi wani tasiri na musamman a zukatansu tare da ƙawatata a cikin idanunsu. A wani gefen sunyi amanna irinta ɗansu ya dace ya samu tun farko, dan ƙarfin gwiwarta sunyi dai-dai da Zawjata-almilk da akafi buƙata ga kowane Shahan-shan. Sannan Malikat da sukema kansu fata. “ALLAH yay miki albarka”. Suka faɗa kusan a tare su duka huɗun. A kan laɓɓanta ta amsa da amin. Sun cigaba da tattaunawar da gaba ɗaya ta saka Iffah cikin ƙagara, ƙagara mai nasaba da shiga ruɗanin wani furici daga Daneen Ammarah. Wai jiya Shahan-shan ne wanda ya ziyarcesu a wannan falon, tana buƙatar samun filin tunani dan zuciyarta da ƙwaƙwalwarta fa gaba ɗaya sun kulle, ruɗani ya gama mamaye duk wani hangenta da dama bai wuce iya tsayin ƙafafunta da shekarunta ba.... ★★.... A hankali ta maida ƙofar ta rufe tare da jingina a jikinta ta lumshe ido da sauke numfashi tamkar mai kokawar jawosa. Shin murna zatayi a wannan gaɓar ko kuwa shiga ruɗani?. Idan ance Shahan-shan ne a jiya ta yarda, shi kuma wanda tai gamo da shi a mabanbanta wajeje kafin shigowarta masarauta wanene shi?. Wannan tambaya tafi kowace tambaya girma da girgiza zuciyarta a duk abubuwan dake cin ranta. “Kai nifa nama ruɗe wlhy”. Ta faɗa a zahiri tana zamewa cikin sarewa ta zube ƙasa. Ta jima a wajen cikin halin shiru da ambaton hasbinallahu wa ni'imal wakil ko zata samu dai-daiton komawa cikin hankali dan da gaske komai na halittarta mai motsi ya raunana da rauni mafi ban tsoro da shiga ruɗani. Tsahon lokaci ta kwashe a wajen tana kokawa da raunin zuciyarta da rashin ƙarfin gudanar jini. Fahimtar wancan tunanin na buƙatar lokaci ya sata turesa ta maida hankali akan tattaunawarsu da su Malikat. Tabbas wannan shine babban ƙudirinta dayin ƙundunbalar juriya na tunkarar rayuwar da bata da tabbacin tsallakewa. Duk da tasan anfi ƙarfinta, dama duk wani mai ƙarfi da take kallon ƙarfinta ta zaɓi fuskantar mutum mafi girman iko da tsaro domin ɗaukar fansa. A kwanakin da suka gabata na kasancewarta cikin wannan daula ta fara fidda ran samun cikar burinta saboda dalilai masu yawa. Ciki harda rashin samun koda ƙanƙanuwar ƙofar sanin minene ma daular ruman ɗin ta ƙunsa balle Shahan-shan da kansa. Sai gashi a yau cikin sauƙi an buƙaci kaita inda zuciyarta ta fara raya mata zuwansa ba ƙaramin tsalle bane da ba'a da tabbacin fita idan an shiga, aka kuma sanar mata wani yanki na sirrin daular ruman mai girman gaske da ko na ciki basu san da shi ba ƙila. “Anya babu wani abu a ran mutanen nan saɓanin abinda suka faɗa?” bakinta ya furta a zahiri cikin sake dulmiya a ruɗani. (Koda akwaisa yardar ki dasu ce zata baki ilimin sanin hakan) zuciyarta ta faɗa cikin ƙarfafata da ture raunin dake neman rinjayarta.... Knoking ƙofar daya wanzu a dai-dai lokacin ya sata jan numfashi a sauƙaƙe. Da ƙyar ta iya miƙewa daga zaman daɓaron da tayi ta buɗe. Daneen Ammarah ta sakar mata murmushi. Cikin yaƙe ta mayar mata da murtani da matsawa ta bata hanya. Rissinawa hadimar da suke tare tai ta gaisheta, hannu kawai ta ɗaga mata alamar amsawa tana bin ledar hanunta da kallo...... ★★.... ★.... ★★..... Kamar yanda aka sanar da Barrister kai tsaye station ɗin da akace su Babiy suke suka nufa. Kasancewarsa babba kuma sananne basusha wahalar ganin ogan station ɗin ba kai tsaye. Sunyi gaisuwa irin tasu ta manyan ma'aikata, su kai kuma gaisuwar girmama juna da su Kaka. Barrister ya gabatar da kansa, ya kuma gabatar da abinda suke tafe da shi harda hoton su Babiy domin sauƙaƙawa. Jami'in yay shiru yana kallon hotunan kamar mai hasashe, sai kuma ya ɗago ya kalla Barrister “Gaskiya banajin akwai waɗan nan mutanen a wannan station ɗin Barrister”. Barrister daya fahimci matsala ce ke neman shigowa yay ɗan murmushi da muskuta zamansa. “Yallaɓai adai sake dubawa, zata iya yuwuwa ko akwaisu ɗin baka da labarin hakan. Amma tabbas suna a wannan station ɗin. A matsayina na Barrister ba nazo nan dan a bani belinsu bane ba, duk da nasan basu da hannu a abinda ake zarginsu. Nazo ne dan na gana da su, sannan a miƙasu kotu saboda nasan dai ita matar data saka aka kawosu nan burinta a kwatar mata hakkin mijinta”. “Iya gaskiyata nake faɗa maka Barrister babu waɗan nan mutanen a wannan station ɗin. Amma mizai hana ku sami ita matar na tabbata tunda tare da ita akaje tasan wane station ne”. Barrister yay shiru yana kallonsa cike da nazari. Hakama Kaka da Abu Zainab. Kusan minti biyu shiru babu wanda ya motsa, kafin Barrister ya miƙe yana ɗan murmushi ya bashi hannu. Suma su Abu Zainab miƙewar sukai... Da kallo ya bisu har suka gama ficewa, ya kai hannu kan wayarsa dake saman desk ɗin sa yana wani murmushi. A bugu biyu aka ɗauka wayar daya kira. Sallama kawai yay da faɗin, “Kamar yanda kai hasashe ranka ya daɗe yanzu suka bar office ɗina”. Shiru yana sauraren mi'ake faɗa daga can, sai kuma yay murmushi da amsawa da “Angama ranka ya daɗe”. Daga haka ya ajiye wayar yana wata ƴar iskar dariya... Abu Zainab daya kasa fahimtar komai saɓanin Kaka da Barrister dake hangen wani abu dalilin kashedi da akai musu kafin zuwansu nan dama ya katse shirun da motar ta ɗauka ta hanyar nisawa. “Anya kuwa wannan jami'in akwai gaskiya a maganarsa Barrister. Kagafa yanda yake ƙyaf-ƙyaf da idanu kamar tsohon ɗan jari hujja. Nifa wannan al'amari ya fara bani tsoro wlhy”. Barrister da zuciyarsa ke kai kawo ya fesar da huci, “Kana tunanin yaƙi faɗa mana gaskiya ne Zakariyya?”. “Fuskarsa ta nuna hakan ai Barrister, ko kuwa Kaka?”. Kaka da shima dai yake aune-aunensa a rai ya girgiza kansa. “Zata iya yuwuwa gaskiyar ya faɗa, sai dai kumin wani taimako ɗaya dazai warware mana gaskiyar tasa ko saɓaninta, bayan nan zan sanar muku abinda ya faru kafin zuwanmu nan”. Barrister da shima abinda ke'a ransa kenan ya ɗan juyo ya kalla kaka ta madubi, “Muna jinka Baba”. “Muyi gaggawar isa gidan Dawood”. “Shawara mai ƙyau Baba”. Barrister ya faɗa yana juya motar hanyar da zata kaisa gidan Abu Moosa. ★★... ★★... ★★... “Mamy kuma duka wayar da lap-top ɗinne nawa?”. Iffah ta faɗa da mamaki. Murmushi Daneen Ammarah tayi, “Ibnati wannan ai ba komai bane ba, sannan ko baki faɗa ba kina buƙatar su tare da ke kodan ki dinga jin motsin gida. Na biyu kuma wannan aikin da zaki fara kowa yasan mai haɗari ne, dolene ki kasance da waya a duk inda kike a masarautar nan. Da zarar Kinga abinda zuciyarki bata kwanta da shi ba a cikin mu huɗun zaki iya kiran kowa ki sanar masa. Lap-top kuwa ni naga ya dace na kawo miki ita domin ɗebe kewa. Amma kiyi taka tsantsan ki kuma kula sosai, dan samun waɗan nan na nufin zaki iya mu'amula da kowa musamman a yanar gizo batare da kin samu tabbacin wanene ɗin ba”. “Haka ne Mamy, insha ALLAH zan kiyaye. Nagode sosai ALLAH ya saka da alkairi”. “Karki damu kin cancanta ne ai”. ★Iffah ta daka tsallen murna bayan ficewar Daneen Ammarah, harda ƴar rawarta. Duk wani tunani da kaikawon da zuciyarta ke mata akan Shahan-shan zuwan wannan waya da lap-top ya kauda mata shi. Domin a ganinta dama biyu ce tazo mata a lokaci guda kuma zata damata ta yanda dole sai Shahan-shan ya shata. Yanzu dai abu na farko da zata fara shine malam Fawzan. Ta tura masa saƙo bayan nemansa da tai shi da abokinsa wayar Arfa dake hanunta ta mutu ba caji, tana buƙatar tasan ko yaga saƙon? Ya kuma iyayenta suke?. Samun wayar da caji yasa tun a daren ta haɗata, duk da taga akwai sim card batai amfani da shi ba ta cire na Arfa ta sanya. Tamkar jira saƙon Malam Fawzan ne ya fara shigowa, jikinta har tsuma yake wajen buɗewa. Batako kai ƙarshen karantawa ba kira ya shigo. Gabanta ne ya faɗi ganin baƙuwar lamba, amma tsabar ƙarfin hali sai ta ɗaga. “Sir!”. Ta faɗa cikin gwalalo idanu da nufar ƙofa da sauri ta saka key. Daga can aka amsa mata da “Na'am Fareedah. Ina kika shiga haka? Tun bayan ganin saƙonki na kasa samunki, har zuciyata ta karaya da ko wani ya gano ki ne?”. “Babu wanda ya gano ni Sir, akasi aka samu wayar ta mutu, na kuma rasa ta yanda zanyi cajinta dan na manta da cajan a gida”. “Ayya. Kin ganni akoda yaushe cikin gwada wayarki nake koza'a dace. Saboda ke na samar da wannan layin na sirri. Yanzu ma gwadawa kawai nake amma banyi tunanin samunki ba sam”. Iffah ta share hawayen da suka silalo mata tana ɗan murmushi. “Nagode Sir, koda banyi nasara ba bazan taɓa mantawa da kai ba. Ina fatan ka bincika min su Ummu. Dan sam na kasa samun kwanciyar hankali na rashin jin su”. Ɗan jimm yay kamar mai tattaro abin faɗa, sai kuma yay ɗan murmushin basarwa. “Suna lafiya dan har gida naje, sai dai ban samu shiga ba kasancewar suna tare da tsaron dakarun masarautar har yanzu. Amma nayi ƙoƙari mun haɗu da Hanash....” “Amma miyasa wayoyinsu basayi?”. Ta katsesa a ƙagauce. Da ƙyar ya iya tattaro abin faɗa a wannan gaɓar ma. “Shi Babiy wayarsa ta samu matsala ne. Hanash kuwa network ne dan yace min shima yasha nemanki amma baya samunki”. “Bani da lafiya ne, ba koyaushe kuma wayar ke kunne ba. Amma yanzu zan sake nemansa insha ALLAHU dan ina matuƙar bukatar son naji muryoyinsu kozan samu nutsuwa”. “Hakan yana da ƙyau. ALLAH kuma ya ƙara lafiya. Kinyi waya da abokina kuwa?”.. “Eh nayi, amma kamar yanda na sanar maka a text message an ɗaga amma ana mun wani shirmen banza. Daga ƙarshe ma akace wai na saɓa lamba”. Karan farko malam Fawzan yay ƴar dariya. “Taku ne kawai irin na masu iyawa. Amma a yanzu na tabbatar zai saurareki”. Iffah ta ɗan taɓe baki kamar tana gabansa. “Ni ALLAH harna ɗauka ko ka yaudareni ne ka bani number daba itaba ma”. “Iffah koda abin wasa kikazo da shi bazan masa riƙon banza ba balle wannan mai matuƙar muhimmanci da ma'ana. Yanzu dai ina fatan wayar taki akwai caji?”. “Ai bama waccan bace, sabuwa fil aka bani a kwali yau harda lap-top”. Jimm yay na wasu ƴan sakkani. Sai kuma ya cire wayar a kunnensa ya duba. Tuna ashema shine ya kirata ya sashi sake maidawa. “Amma baƙya zargin akwai wani dalili a baki wayar? Mutanen nan fa sunada haɗari sosai Iffah. Bazan ɓoye miki ba inajin tsoron ƙarfin ikonsu”. “Nice zan baka wannan labarin Sir kasancewata a cikinsu yanzu. Sai dai kuma wanda suka bani wayar yanki ne na mutanen kirkin cikinsu. Kasan a ko ina akwai ƙyakykyawa akwai kuma mummuna”. Tsaf ta kwashe yanda sukai ta sanar masa saboda ta matuƙar yarda da shi. Shine kuma takema kallon wanda zai taimaka mata a wannan yaƙin kamar yanda tai fata. Ya jimanta al'amarin matuƙa, ta wata fuskar kuma yayi murnar ganin hanyar samun nasararsu ce tazo. “Lallai mun samu hanya ta jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya Iffah. Sai dai dole kiyi taka tsantsan da waɗan nan wayoyin. Ki buɗe account da duk kike ɓuƙata da layin da suka sanya miki, shi kuma wannan nakin watsap kawai zaki buɗe da shi, sai dai karki barsa akan wayar, da kuma kinyi magana da Ajmaal da shi ki goge watsap ɗin ki cire layin sai zaku ƙara ki maida. Akoda yaushe wayarki ta kasance da security na idanunki bana wayar ba. Dan inada tabbacin suma zasu saka ido a kanki. A daren nan ki buɗe watsap ɗin ki sake ma Ajmaal magana”. “Nahode Sir, insha ALLAHU zan yi duk yanda kace”.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_29_* .........Barrister na ƙoƙarin shiga layin gidan Abu Moosa wata baƙar mota na ficewa. Babu wanda ya damu da ganinta a cikinsu, suka ƙarasa kutsa kai har ƙofar gidansa. Ganin gidan rufe daga nesa baisa sun kawo wani abu a ransu ba duk suka fita. Abu Zainab ne ya ƙarasa har jikin ƙofar. Kansa tsaye ya kai hannu ya fara knoking, amma har tsahon mintuna biyu babu alamar motsin mutum. Juyowa yay ya ɗan kalli su Kaka dake kallonsa. Cikin sarewa ya girgiza musu kai. “Banajin fa akwai mutum a gidan nan, dan babu wani motsi”. “Kara dai bugawa”. Cewar Barrister cikin bashi ƙwarin gwiwa. Kai Abu Zainab ya kaɗa ya cigaba da bugawa, maimakon a buɗe nan sai ƙofar makwaftansu ce ta buɗe. Wani matashin saurayi ya fito. Abu Zainab ya maida hankalinsa garesa suka gaisa. Kafinma ya tambaya saurayin ya bashi amsa. “Ai banajin akwai kowa gidan nan. Saboda yanzu babu jimawa matar gidan aka ɗauke a mota harda ƙaton akwati”. Da mamaki Abu Zainab ya ce, “Kana nufin yanzun?”. “Eh, dan banajin sunma rufa minti goma. Ta kuma yima mahaifiyata sallama akan zata koma garinsu ne. Harma mukayi mamakin hakan ganin duka rasuwar mijinta bai wuce kwanaki goma sha biyar ba”. Godiya Abu Zainab yay masa jiki a saɓule ya koma gasu Kaka. “Waifa kunji babu jimawa tabar anguwar nan. A yanda tacema makwaftansu ma ta koma garinsu ne”. “Garinsu kuma?”. “Haka dai yace. Nifa na fara tsorata da lamarin nan, dan tabbas akwai abinda ke ɓoye da bamu sanshi ba”. Tsakanin Kaka da Barrister babu wanda ya iya cewa komai.... *_MASARAUTA (JASRAH)_* “Wai ni naga sai faman moso kike, kinma kasa bani labarin yanda kukai da Akia akan zancenmu na jiya. Kuma naga wucewarku ke da ita ɗazun zuwa sashin Mamma (Malikat Haseena)”. Cike da zolaya ta ɗan hararesa. “Ko kuma dai ƴan leƙen asirinku sun sanar maka ba”. “Leƙen asiri kuma? Haba sai kace dai ku. Kudai matan masarautar nan ne dai da baƙwa iya rayuwa sai dai ƴan leƙen asiri. Amma mu maza miya haɗamu da wani leƙen asiri kamar marasa aikin yi”. Ta ɗan dara kaɗan da taɓe baki. “Muma ɗin ba kowa ne yake hakan ba kamar yanda kuke zargi. Niko waya dameni a daular nan dahar zan damu da saka wani bibiyarsa. Ko lamarin Zaki addu'a ce tamu a garesa kawai”. “To ALLAH yasa hakan. Yaya zaman naku ya kasance?”. “Zama an samu nasara. Dan inama Akia bayani a take ta amince, ta kumace muje sashen Mamma itama muji ta bakinta. Alhamdullah sai aka dace itama zancen ya ƙayatar da ita. Na taƙaice maka zance a yanzu haka ma mun zauna da ita yarinyar. Insha ALLAHU zuwa gobe ma zata koma sashenta. Sai dai abu ɗaya ne fa Mamma bata amince da shi ba”. “Minene shi?”. “Sake kai wata Zawjata-almilk turakarsa. Acewarta za'a ƙara jinkirtawa aga abinda yarinyar zata samo. Sannan za'a sakema duka Zawjata-almilk ɗin sabon horo akan kasancewar su Zawjata-almilk a wannan karon”. (Wata sabuwa kenan, wannan tsinanniyar tsohuwar ko) ya ambata a zuciyarsa. A fili kam fuskarsa ya kawata da sabon murmushi da faɗin, “Woow wannan tsarin yayi, shiyyasa Mamma ke daɗa birgeni. Hakan ma wani mataki ne da zai taimakemu matuƙa. ALLAH kuma yasa mu dace”. “Amin dai Abu Harith. Dan gaskiya a wannan gaɓar ina tsoron a ce abinda ya faru ya sake maimaita kansa. Saboda zuwa yanzu hankalin manyan ƙasashen duniya ya fara dawowa kan ƙasar ruman. Dan ma ana shakkarmu ne da tuni wani zancen ake ba wannan ɗin ba. ALLAH dai ka bayyana gaskiya ka kuma wanke wanda ake neman disashewa saboda son zuciya”. “Amin Meera. Amma ko yanzu ɗin ma akwai abinda baku sani ba. Shahan-shan na ɓoyewa ne kawai dan karya tashi hankalin kowa. A wata mai kamawa shugabannin manyan ƙasashe bakwai na africa zasu kawo ziyara ƙasar ruman. Bisa jagorancin shugaban ƙasar Nijeriya, bama raba ɗayan biyu akan wannan al'amarin ne kuma”. “Ya Arrahaman”. Jasrah ta faɗa a tsorace. “Ki kwantar da hankalinki, dan ALLAH kuma kar kowa yasan wannan, dan na sanar miki ne kema saboda na yarda da ke”. Badan hankalin nata ya kwanta ba ta jin jina masa kanta kawai. Cigaba da kwantar mata da hankali yay cikin kwantar da murya har barci ɓarawo ya kwashe ta. Sai da ya tabbatar barcinta yayi nisa sannan ya zare jikinsa cikin sanɗa ya fice zuwa ɗayan ɗakin dake jikin wanda suke kwance da waya a hannunsa...... *_ZAWJATA-ALMILK_* Dukan matakin shawarar da Sir Fawzan ya bata shi tabi, dan tunda sukai bankwana da Daneen Ammarah tai shirin barci ta sakama ƙofarta key. Ta fara da buɗe Watsap, sannan ta lalubo number Ajmaal. Cikin sa'a kuwa yana online, wani farin ciki ne ya ratsata. Taja kakkauran numfashi da godema ALLAH. _Assalamu alaikum_ Ta fara turawa da fatan samun amsa zuciyarta na harbawa da sauri-sauri. Tsahon mintuna kusan goma babu alamar zama a buɗe saƙon. Sake tura sallamar tayi a karo na biyu. Ta dasama wayar ido kamar mai irgan fitan numfashinta. Kamar a mafarki taga an buɗe, tai kasare tana jiran taga an amsa sai dai shiru har kusan wasu mintuna goman. A yanzu kam zuciyarta ta sosu, dan duk yanda take buƙatar abu ga mutum ta tsani a wulakantata. Ta cije lips da ƙarfi tana danne fushin dake son mata tasiri. _Wa'alaikissalam_. Aka amsa mata a bazata. Nannauyar iska ta furzar, itama ta buɗe saƙon ta share. Da ƙyar ta iya danne zuciyarta mintuna bakwai suka cika. _Sunana Fareedah bint Zayyan_. Tsahon mintuna kusan goma yanzu ma sannan aka buɗe. _Na sani_. Tai shiru tana kallon amsar, sai kuma taja tsaki na takaici. A fili ta furta, “Aikin banza. Ka sani shine baka san aikinka ba mtsoww!!”. Sharewa tai, ta rubuta masa. _Kwanaki na kira, amma akaimun tarbar da har yau ina mamakinta. Shin dama manyan ƴan jarida haka suke da wulaƙanta bukatar marasa ƙarfi?_ Tsahon minti ashirin da buɗe saƙon babu alamar za'a amsata. Hakan yay mata ciwo matuƙa. Sir Fawzan ta kira, bugu biyu kuwa ya ɗaga. A ɗan rikice yace, “Iffah baki ganin akwai matsala yawan kiran nan? Masarauta fa ba irin ko'ina bane sunada hanyoyin tsaro ɓoyayyu ciki harda cctv”. “Hakane Sir, amma nima dole ce ta sakani kiran. Anya kuwa wannan abokin naka da gaske ɗan jaridar ne? Sam baya ɗaukar al'amarina da muhimmanci, duk ɗan jarida na kwarai zaka samesa da zumuɗi akan labari, musamman ma irin nawa daya kasance babba”. “Miya faru? Bai amsa saƙonki ba ne?”. “Ya amsa. Amma yanamun yanga. Harna fara jin gundira a huɗɗa da shi”. “Karki saurin karaya, amma nayi mamaki dan masan Ajmaal ba mutum bane mai irin wannan siffar wlhy. Inaga dai akwai aikin da yake yi a wannan gaɓar shiyyasa. Kin san su abubuwan nasu da yawa. Kin san kuwa yanda ya ƙagu akan son jinki, dan ɗazun na fara ƙyara masa abinda ke ranki kaɗan”. Ta ɗanji sassauci daga haushinsa. Taja ajiyar zuciya a fili da faɗin, “Shike nan bara na koma”. Sallama yay mata ya yanke wayar. _Am sorry na haɗa wani aikin ne da saurarenki. Yanzu ina jinki_. Da wannan saƙon taci karo bayan yanke wayar. Sanyi ta ƙaraji a ranta. Cikin ɗan karsashi ta maida amsa. _Ayya kayi jaƙuri na maka gurguwar fahimta._ _Babu damuwa_ Aka amsa mata cikin ƴan sakanni. Cike da karfin gwiwa ta rubuta. _Nasan abokinka ya fara maka bayani akan nemanka da nake ido rufe._ _Hakane. A yanzu haka ma munyi dashi zai bani wani yankin rubutunki dake hanunsa._ _Alhamdullahi. A yanzuma akwai cigaban wancan rubutun a hannuna nima. Sai dai ban san ta hanyar da zai zo garesa ba ko gareka_. _Wannan mai sauƙine ai. Zaki iya turamin shi tanan_ _Wai! Amma typing ɗin zaimun wahala gaskiya_. _Karki damu ki ɗauki hoto_ Cike da zumuɗi ta miƙe. Gado ta ɗaga ta ɗakko notebook ɗinta, a take ta ɗauka hoton duka rubutun ta tura masa. _Gashi, insha ALLAHU duk bayan kwanaki uku zaka iya ganin saƙona_ _Masha ALLAH hakan yayi, sai dai a maimakon kwana uku mizai hana muyi mako-mako. Dan wani abun da zai zo yana buƙatar bin diddigi da faɗaɗa bincike mu tanan a garemu._ _Yanda kace haka za'ayi. Ni dai fatana ka kasance ɗan jarida mai gaskiya da riƙon amanar kimar ƙasarsa. ALLAH shine shaidata na baku dukkan yarda kai da Sir Fawzan. Idan akasin nasarata ya biyo bayan yunƙurina ku zan zarga. Duk kuma yarinyar data samu kanta a irin halin da ƴan uwana da ni muka kasance kuma zaku amsa sunan azzalumai ne kamar yanda Shahan-shan ɗin ke amsawa a yanzu. Ku kuma dinga tunawa da mala'iku tare da ku masu rubutawa daga ayyukanku na zahiri da baɗini. ALLAH ya cigaba da tsare ƙasar ruman. Idan kanada wata tambaya zaka iya tura min text message na Barka lafiya_. Bata jira amsa daga garesa ba ta fita gaba ɗaya. Watsap ɗin ta goge ta kashe wayar gaba ɗayama tana sakin ajiyar zuciya a jajjere. Sai takejin wani kaso na damuwarta da nauyin zuciyarta ya ragu kaɗan. A wani gefe kuma kamannin mutumin can da wanda ta gani a jiya matsayin Shahan-shan ne ke ta faman mata kaikawo babu alamar zai barta ta huta...... ★★.... “★★” .....★ “Lafiyarki da tsahon zamani su da ɗa tabbatuwa uwa mai share kukan masu kuka”. Ta-kurya dake kai gwuyawunta ƙasa ta faɗa sakamakon zuwan Uwa gareta a bazata. Kamar ko yaushe, cikin shigarta ta jajayen kaya, ta gyara zaman ƙasaitar ta. Ƙoƙon dake hanunta ta miƙama ta ƙurya. Hannu biyu ta karɓa, ta kafa kai ta shanye abinda ke ciki. “Tukuycin cika umarninmu na yanka babbar baƙar dabba da kikai ne. Azamarki da himmarki zaisa bazaki taɓa nema daga garemu ba ki rasa Ta-kurya (Wa'iyazubillah 😭). “Nagode uwa mai share kukan masu kuka”. Murmushin daya sake munana fuskarta ta saki tana ƙara kalmashe ƙafafu a kujerarta. “Karki damu ke mai nasara ce. Minene makomar ayyukan da muka barki da su?”. “Ina kan yunƙurin ƙarasawa. Na kuma samu ƙyaƙyƙyawan labari a majiya mai ƙarfi yarinyar zata koma sashenta. Sai dai akwai zaman sirri dasu Uwar masu gida sukai wanda babu wanda yasan misuka tattauna. Ina dai ƙyautata zaton duk akan komawar yarinyar ne”. “Kar tattaunawarsu ta dameki. Tabbatar da ƴan leƙen asirinki cikin hadimanta shine aikinki na gaba. Dan kunada yawa masu wannan burin kema kin sani basai na sanar miki ba. Ina kuma tunatar dake rigar can dake a sashen Uwar masu gida. Da zaran ta tare ki kasance ɗaya daga cikin masu janta a jiki. Yardarta gareki ne zai bamu damar amfani da ita wajen cikar burinmu”. “Na gode da kasancewar ki haske mai haskamin duk wani surƙuƙin da zai iya zamemin duhuwa uwa”. “Biyayyarki garemu ita ce tushen share kukanki Ta-kurya. Dan haka bazamu taɓa barin kiyi kuka ba maƙiyanki suyi dariya ba. Sai dai su suyi kuka ke ki kasance cikin dariya a kullum bisa nasararsu. Karki shagala ƴar shilar suda nada taurin kai, Karki zama cikin jerin mutane masu raina allura ta zame musu garma. Muna son tasha madarar nan a ƙalla sau uku daga gareki da zaran ta tare a sashenta”. Ta ƙare maganar da miƙama ta ƙurya ƙoƙon da bata san daga ina ya fito ba. Dan ganinsa kawai tai a hannunta tamkar ƙyaftawar idanu. Hannu biyu tasa a wajen amsa tana jera mata kirari da godiya. A hankali ta fara disashewa a idanunta tamkar baƙin hadarin da masha ruwa (Bakan gizo) ya shanye cikin sakanni. Ta-ƙurya ta sauke nannauyan ajiyar zuciya. Sai kuma ta miƙe da ƙoƙon da Uwa ta bata. A guri na musamman da na'urar sanyi ke aiki ta ajiye madaran, murmushin jin cigaba da tabbatuwar nasararta na cigaba da ƙawata ƙyaƙykywar fuskarta. Ji take a ranta yanzu ne fa za'a fara wasan na gaskiya. Dan dama idan aski yazo gaban goshi masu iya magana kwance yafi raɗaɗi da zafi. Ta jima bata samu irin wannan damar ga uwa ba a ɗan tsakanin nan da mafi yawan lokuta sukafi ganawa cikin ɓacin rai da rabuwa da ɓacin ran. Amma a yau yanda uwa ta ziyarceta ya sakata jin karsashi da ƙarin kwarin gwiwar cigaba da ruguza duk wanda ya cigaba da yunƙurin shiga gaban nasararta.......✍️ “Humm masu karatu, da gaske fa yanzu ne za'a fara wasan na gaskiya. Ga dai Iffah zata koma ɗakinta. Komawar dake cike da burikan wasu dake zagaye da ita. Buri kuma irin wanda ke kamanceceniya da juna ta fuskar wanzuwa. Manufa kuma kowa da irin tasa. Ita kanta Iffah da nata ƙudirin karku manta. Shin wanene zaiyi nasara ne? Yaya batun su Babiy kuma? Dan maimakon haske komai ƙara cuɗewa yake. Kaka zaiyi wani yunkuri a alamarin kokuwa Barrister zai janye bisa gargaɗin da akai masa shima?. Kumuje zuwa dai dan ba'a fara komai ba sai yanzu😉🥱”. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_30_* ........Kamar yanda su Malikat Haseena suka faɗa a yau aka tashi da gyaran sashen Iffah, sai dai abinda ya Bama kowa mamaki ba inda aka fara kaita bane. Ɗaya daga cikin sabbin sashen da babu wanda ya taɓa rayuwa a cikinsu ne a masarautar. Hasalima an jima ana gutsiri tsomar dalilin gininsu da Tajwar Eshaan yasa ayi batare da ansan dalilinsa ba. Ba kayan ƙawata gida kawai aka zubama sashen ba, harda tarin sitturu da kayan ado na sakawar Iffah. A karan kanta kuma masu gyaran jiki na musamman ne suka duƙufa kanta a yinin wannan rana. Da dare ta samu hutawa. Washe gari aka cigaba da mata gyaran da ita kanta sai da zuciyarta ta fara shiga wasi-wasi. Koda yake dama a ciki take. Dan gaba ɗaya kwanakin nan aikinta kawai shine nazari da fasalta abubuwa masu yawa a rai da takasa gane bakin zarensu sam. Sai dai shawarar malam Fawzan ta waccan ranar ta ƙara mata ƙwarin gwiwa da maidota a hayyacinta da matsayin shigowarta daular ruman..... Tsahon kwanaki uku ta gyaru ta ƙara ƙyau tamkar ba'ita tayi fama da jiyya na a kwanakin baya. Ƙamshin dake fita a jikinta ma kawai ya isa ai kiransa na musamman. Ita a karan kanta har gizago canjawar tata ke mata. Jikinta ya murje ta ƙara girma da cika ido tamkar ba autar Ummu da Babiy ba. Ga wani jin kai da takejin ta ƙara masu neman kere shekarunta. Babu shakka kuma hakan nada nasaba da girman da ake bata. Masarauta da jama'ar cikinta zance ya yaɗu yau za'a maida Zawjata-almilk sabon sashenta tunda ta samu sauƙi. Shaidar haka kuma nada nasaba da walimar da Malikat Haseena suka shirya, acewarsu ta aure ce da ba'aiba sanadin abinda ya faru za'ayi yanzu. Shirya wannan walima ya kawo ƙananun magana matuƙa, dan kuɗi aka kashe tamkar za'a sake wani sabon auren. Abin mamaki sauran mata biyu kafin Iffah ga Tajwar Eshaan sai al'amarin ya sosa musu zuciya duk da har yanzu zaune suke batare da ko Tajwar ɗin sun san kalarsa ba. Sam Iffah bata san da wani taron walima ba, sai da aka kammala mata shiri cikin wasu ƙawatattun kaya masu tsananin ɗaukar ido da tabbatar da ita amarya ta gaskiya mai amsa sunan Zawjata-almilk kanta ya fara ɗaurewa. A ganinta in har shigace ta iya rakata sashenta baici ace ta ƙawatu har haka ba kodan kasancewar dare ne ma. Kai mutanen nan fa sun fara caja mata ƙwaƙwalwa, ta faraji a ƙasan ranta akwai manufa. Amma dai koma minene zata jure har zuwa lokacin samun ƴancin kanta na komawa sashen nata dan ta shiryawa kowa talalarsa. A kwanakin baya ta kwantar da kai ne ga kowa domin fahimtar manufar wasu koda kalilanne a cikinsu. Alhamdullah kuma ta dace, dan koba komai ta gama samun yardar Daneen Ammarah da masu gayya da aiki Malikat Haseena da Malikat Bushirat. Duk da dai tasan kada mage ba yankata bane. Amma koba komai raina allura yakan sa ta zama garma ga wanda yay sakaci ai. Taji ba daɗi da barin ɗakin data rayu tsahon kwanaki cike da kewa. Koba komai bazata manta da rayuwar kusan sati uku da tayi a cikinsa ba. Ta koyi ilimi da yawa, harma da darasi data ɓoye matsayin sirrinta. Da wannan tunanin a ranta har aka iso babban ɗakin taro na cikin masarautar, wanda ya ƙunshi duk wani babba mai faɗa aji. Al'ajab ya kama Iffah, amma ta dake zuciyarta na sake tauri na nan dalilin ɓoye mata wannan zaman da akai. Amma a zahiri rashin ƙarfin cewa yasata yin luff kamar yanda ta kasance a kwanakin da suka gabata na samun lafiyarta. Daneen Ammarah data kasance mata ƴar jagora kasancewar fuskarta a sakaye take ta kaita har mazaunin da aka tanada dan ita a cikin ƙaton falon bisa tattausar dardumar da aka shirya walimar. Kamar yanda al'adar take, abinci aka fara ci yayinda Iffah ta gagara kai ko ruwan madara bakinta. Yanda tayi ɗin ya sake burge su Malikat Bushirat, suna ji a ransu sun dace da irin surukar da suke fata. Bayan anci ansha kowa ya nutsu. An fara buɗe taron da addu'a, tare da saƙon maraba ga sabuwar Zawjata-almilk, harma da fatan kasancewar ta abinda kowa ke fata. Kowa dai ya amsa da amin a zahiri, a baɗini kam sanin sirrin wasu sai ALLAH. A mataki na biyu shine zagayawa da Zawjata-almilk takai gaisuwa ga duk wanda ke wajen, kasancewar kakanni ne makusanta da iyaye, da yayye. A yanzu dai kam da taimakon Jasrah ta motsa, bayan ta janye hular rigar alkyabbar jikinta data hana kowa kallon ainahinta a tun farko. Duk da Iffah taji ta takura, hakan wata damace a gareta na sanin dukkan masu faɗa ajin, zai kuma zama jagoran abinda zai taimakawa nata ƙudirin. Idanunta suka cika da hawaye, a lokacin da take durƙushe gaban Malikat Haseena matsayin bankwana. Tanajin tsohuwar a ranta, ta kuma samu wani kebantaccen ilimin zamantakewa da ita. Ta saka mata albarka tare da yaba ƙyawawan halayenta da jinjinama iyayenta tarbiyyar da sukai mata. Ta ƙare da fatan alkairi da samun zuri'a mai albarka tsakaninta da Shahan-shan. Waɗan nan zantika sun zama abin kaiwa da komawa a zukatan manyan masarauta. Dan kowa na ganin kamar wata isharace Malikat Haseena ta isar cewar ta karɓi Iffah ɗari bisa ɗari matsayin Zawjata-almilk fiye dana baya da suka gabata. Iffah a karan kanta taji tausayin tsohuwar bisa ƙudirinta na shigowa daular ruman data tabbatar yasha banban da fatan da Malikat Haseena tayi gareta a yau gaban duk wanda ya isa a ƙasar ruman ma ba daular ruman ɗin kawai ba. Har yanzu har gobe da jibi tana akan bakanta na ɗaukar fansar rasa ƴan uwanta. Abin harinta kuma ɗaya ne tal shine Tajwar Eshaan, inma da wanda zasu biyo bayansa sai ta gama da babban dodon nasu. Ta samu ƙwarin gwiwar hakanne da tabbacin jin sai an kai matan turakarsa ake fiddosu babu rai. Sai kuma bincike da shaƙiƙansa guda huɗu sukai yunƙurin ɗaurata a yanzu haka. Kenan babu buƙatar wasi-wasi koma minene shike ƙullasa... Malikat Bushirat ma tayi irin makamancin addu'ar Malikat Haseena ne ga surukar tata. Ta ƙara da faɗin ita ɗiya takejin ta samu ba Suruka kawai ba, tana kuma fatan ta kasance kibiyar ajali ga masu ƙudirin sharri a ciki da wajen daular ruman. Tabbas maganar Malikat Bushirat tafi ta Malikat Haseena ɗumama zukatan wasu, yayinda mugun ƙudirinsu akan Iffah ya ƙara hauhawar farashi a zukatansu, amma duk sai suka ɓoye suma sukai mata irin tarbar data ɓoye dukkan ainahinsu. Dan Miran Jasim ma da akazo kansa har ƙyauta ta musamman ya gabatar ga Zawjata-almilk. Iffah data kasance cikin ladabi da ƙawata harshenta gaban kowa yayin miƙa gaisuwarta duk da ƙarancin shekarunta kaifin basirarta da wayonta ya bata damar nazari da adana cewar kowa a wajen da fuskar daya tarbeta ta hanyar kallonsu a ƙyalkyalin jikin rigarta datai matuƙar taimaka mata harta ambata godiya ga Malikat Haseena data zaɓa mata rigar domin sakawa a yanzun. Ba kalaman kawai ta riƙe ba da fuskokinsu da suka fita tartar bisa taimakon hasken kwayayen wutar lantarki. Harda sunayensu sun kasance kamar wani zane akan dutse cikin ƙwaƙwalwarta da zuciyarta. Ƙarfe goma da kusan mintuna talatin taron ya tashi na dare, aka fara fita da Zawjata-almilk da kowa ke tunanin sashenta za'a kaita kai tsaye. Sai kuma hakan ya bambanta da tunaninsu a lokacin da Malikat Haseena tabi bayansu akan wheelchair ɗinta matsayin maiyin wannan rakkiya. Abu ne da ba'a taɓa gani ba a masarautar. Dan hatta Malikat Bushirat da Daneen Ammarah sun sake jinjina wannan soyayya mai ƙarfi data shiga tsakanin Malikat Haseena da Iffah. Sai dai hakan ya musu daɗi, musamman Malikat Bushirat da take ganin hakan matsayin ƙarin sanin wanene Shahan-shan a zuciyar Malikat Haseena ga maƙiyanta. A lokacin da kowa ke fitowa daga falon da walimar ta gudana bayan gama sallamar sai da safe gagarumin labari da ɗumi-ɗuminsa shine cin karo da motar data ɗauka Malikat Haseena da Iffah a ciki ƙofar sashen Shahan-shan. A wannan karo hatta da Malikat Bushirat da Daneen Ammarah sai da sukai turus dan shirine da sam basu san da shi ba. A take suka koma ƴar kallo a tsakaninsu, cikin tambayar juna yaya akai haka kuma? Da idanu. Rashin amsa da mai basu amsar ya sasu shanye komai...... ★★.... ★... ★★..... Komai ya tsaya cak a ɓangaren su Kaka a kwanakin nan da suka gabata dangane da neman inda su Babiy suke. Barrister ya sake bin duk hanyar da yake da yaƙinin samu koda na ƙarfin iko ne amma sai ya risketa a toshe. Zuwa yanzu kam su duka ukun sun fahimci komai shiri ne bisa la'akari da labarin da suka bama juna na gargaɗin da akai musu. Sai dai abu mafi ɗaure kai da ban mamaki, wanene mai shirin? A wane dalili yay shirin kuma? Miyasa zaiyi shirin akansu Babiy ɗin?. Waɗan nan tambayoyi sune suka zama abun tattaunawa tsakanin Kaka da Barrister dama Abu Zainab daya saudaukar da dukkan lokacinsa domin ganin komai ya daidaita. Bisa shawarar Barrister Kaka yay shirin komawa Jimna, dan a cewarsa suna buƙatar bada ƙafa kodan harar rayukansu da aka farayi suma. Saboda a kwanaki biyun da suka gabata da ƙyar Barrister yasha a hanun wasu tankunan mai da suka sakashi tsakkiya bisa titi lokacin da yake tashi aiki. Haka yaron Abu Zainab a jiya anyi wuff da shi daga hanyarsu ta zuwa makaranta a cikin ƴan uwansa. Ba kuma a sakesa ba sai a daren jiya bayan sallar isha'i lokacin kowa ya gama jigata da nema da hasashen inda ya shiga. Rubutacciyar wasiƙar da aka haɗosa da shi yayin maidosa ya basu tabbacin daga inda tsiyar take. Kaka ya kammala kulle ko'ina na gidan sannan yay sammala da su Abu Zainab tare da godiya ya ɗauki hanyar inda zai samu motar ƙauyen Jumna. Harya sauka a mototaxi aka dakatar da shi, da mamaki yake duban mai mototaxi ɗin dake miƙa masa ƙaramar jakkar hannunsa. “Baba kayi mantuwa, ALLAH yasa na farga da wuri”. Kafin Kaka ya samu damar cewa wani abu saurayin ya ajiye jakkar gabansa ya koma cikin mototaxi ɗin da baiko waiwayo ya dubi Kaka dake yunƙurin dakatar da shi ba. “Kar kai jayayya tsoho, ka ɗauka dan naka ne”. Aka faɗa ta bayansa dai-dai yana kaiwa duƙe zai ajiye jakar. Ɗagowa kaka yayi, sai dai bayan mutumin kawai ya gani sai ƙurar motarsa. Ran Kaka ya sosu, har fuskarsa ta nuna haka. Alamar ƙosawa da wasan kwaikwayon waɗan nan mutane ya fara tunzura kawaicinsa da son bin doka a yanda tazo. Amma ya fuskanci burinsu kawai su kaisa maƙurar da sai ya gwada ƙwanjinsa akansu. Yay ƙwafa tare da ɗaukar jakar....... ★ “Boss ya ɗauka fa”. Wani matashin saurayi siriri dake zaune cikin taxi nesa kaɗan da Kaka ya faɗa yana ɗan kai hannu a kunensa ya dafe bluetooth ɗin dake manne a ciki. “Tabbas akwai alamar ɓacin rai tattare da shi a yau, dan fuskarsa harta kasa ɓoyewa”. Saurayin ya sake faɗa da alamar amsawa wanda ya kira da Boss ɗin a farko idonsa ƙyam akan Kaka da har yanzu ke tsaye jikin wata mota. Kai ya gyaɗa alamar an sake masa magana daga wayar, sai kuma ya gyara baƙar facing cap ɗin kansa da faɗin, “Eh da alama bai samu motar garin nasu bane. Amma gani ina tunkararsa, komi kenan zan cigaba da riƙe wayar dan kaji komai”. Kaka na shirin ɗaukar jakar da mai mototaxi ya barsa da ita zai bar wajen saurayin ya katsesa ta hanyar masa sallama. A ɗan daƙile ya amsa dan ransa babu daɗi har yanzun. A yanda ya kafe saurayin da idanunsa masu kaifi duk sai yaji ya tsargu. Ya haɗiye yawu da ƙyar cikin ɗan harɗewar harshe yace, “Baba tafiya ne?”. Kaka dake nazartarsa ya ƙyabe baki cikin masa kallon sama da ƙasa yace, “Kaima nasun ne?”. Sai da gaban saurayin ya faɗi, amma yay jarumtar ƙwaɓe fuska da faɗin, “Nasuwa kuma Baba? Ni fa mai taxi ne, na hangokane kawai na iso”. Kaka ya cigaba da masa kallon nazari, sai kuma ya furzar da isaka da kauda kansa yana kallon mutanen daketa faman kai kawo a titin cikin son watsar da lamarin saurayin... “Bar wajen kamar kayi fushi”. Aka faɗa daga cikin bluetooth ɗin dake manne a kunensa........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_31_* .......Takun da baifi uku ba Kaka ya juyo ya bisa da kallo, kamar a bazata saurayin ya tsinkayi muryarsa na faɗin, “Jumna zanje”. Yi yay tamkar bai jisa ba. Hakan yasa Kaka sake ɗaga murya amma ya cigaba da sharesa shima. Yana ƙoƙarin shiga motarsa Kaka daya biyosa a baya yace, “Haba ɗan nan baka jini bane?”. “Sarai na jika Baba. Na fahimci ba tafiyar zakai ba, ba kuma hurimina bane tilastaka”. A karan farko kaka ya saki murmushi. “ALLAH sarki, to ayima tsoho haƙuri ɗana”. “Baba kamin laifin komai ba ALLAH, ai aikina ne. Dama naji kana sanarma wancan ne ni kuma hanyatace shiyyasa ma naje gareka. Zanje ƙauyen Yamanu ne dama”. “A Alhamdullah, lallai hanyarmu ɗaya Bara na ɗakko kayana.” Mutum biyu kawai saurayin ya ƙara ɗauka bayan kaka suka ɗauki hanya. Hakan baisa kaka ya ji wani zargi game da shi ba. Sai ma hira da suka dingayi kai kace sun san juna. Bayan sauke mutum biyun daya ɗakko har ƙofar gida ya kai Kaka. Yaji matuƙar jin daɗin wannan karamci dan haka yay masa tayin shiga ciki yasha ruwa. Saurayin ya ɗan nuna tirjewa amma Kaka ya janye ra'ayinsa a dole ya bisa suka shiga, sai dai dama a ransa hakan yake fata. Ummu na zaune a tsakar gida ita da Iyyani, ta rame matuƙa tayi duhu irin na wanda ya shiga damuwa. Tamkar an sare gwiyawun Kaka ya ƙarasa shiga idanunsa akan Ummu data tsurama bayansa ido. Iyyani ma jiki a sanyaye ta miƙe dan tasan komai tunda kullum sai sunyi waya da Kaka. Itace tai ƙarfin halin masa sannu da zuwa. Ya amsa a sanyaye yana waiga bayansa. “Yaro shigo mana”. Kaka ya faɗa domin samawa Ummu nutsuwa. Da sallama saurayin ya shiga. Ummu tai ƙasa da kanta a hankali. Bayan sun gama zama a tabarmar da Iyyani ta shimfiɗa musu saurayin ya fara gaishe da Ummu. Bata amsa ba, hakan ya sakashi shan jinin jikinsa yay shiru a sanyaye. Iyyani data sake kawo musu ruwa ce ta amsa masa da “Bata magana yaro”. “ALLAH sarki” ya faɗa cikin sauke ajiyar zuciya ita ya gaisheta. Da kulawa ta amsa masa dukkan hankalinta a kan Kaka dake kallon Ummu tamkar ya samu television. Ummu da hawaye suka cikama ido ta miƙe a hankali, ɗaki ta shige duk suka bita da kallo. Kaka baice komai ba hakama Iyyani data zarce kitchen sai gata da kwanon abinci....... ★★... ★★★ ....★ Tamkar raƙumi da akala haka Iffah ke tafiya bisa jagorancin Malikat Haseenat. Kasancewar dare ne babu yawaitar hadimai masu hidima. Sai dai masu tsaro tako ina kai kace zasu iya kare ran wanda suke tsaye a dalilinsa daga ziyartar mutuwa. Tsirarun hadiman da suka samu nata zubewa kwasar gaisuwa, Malikat Haseenat ce kawai ke iya jinsu da ganinsu. Iffah dake ta faman sauke ajiyar zuciya da al'ajabin dukiyar dake narke a wannan gini ji take komai ya ƙwace mata. Ta kasa fasalta komai ta kasa auna komai a ma'aunin rinjayen aikin zuciya dana ƙwaƙwalwa.... “Bismillah”. Malikat Haseenat ta katse mata ɗimuwar da take ciki ta hanyar nuna mata ɗaya daga cikin kujerun katafaren falon mai cike da abubuwan da bazasu lissafu ba. Da gaske Iffah bazata ma iya tantance yanda akai ƙafarta tazo nan ɗin ba. Komai Malikat Haseenat batace ba, dan ta gama karance ɗimuwar dake jagorantar fitar numfashin Iffah. Amintattun Hadiman dake a falon na uku suka zube gaban Malikat Haseenat kawunansu a ƙasa. Hannu kawai ta iya ɗaga musu. Babu buƙatar sai ta faɗa abinda tazo dan shi, shugaban hadiman dake a wannan falon ya miƙe zuwa ga landline domin isar da saƙon zuwanta... “Tsahon rai da lafiya su tabbata ga Uwa a garemu, shugaban na tsumayen isarku a falon sama”. Shiru malikat Haseenat batace komai ba. Yayinda Iffah da zuciyarta ke luguden ke saurarensu cikin juyewar tunaninta da har yanzu bai dawo dai-dai ba. Kusan mintuna uku Malikat Haseenat taima Iffah nuni data miƙe, ita kuma ta birka wheelchair ɗinta suka shiga lifter. Mintuna biyu ne kacal suka iso da su katafaren falon da yafi kowane falo ƙawatuwa a kaf daular ma da sashen kawai ba. Iffah tai ƙoƙarin danne harbawar ƙirjinta sakamakon tozali da wanda ke zaune a falon cikin zama na ƙasaita da izzar masu mulki. Tafiya take tamkar hawainiya saboda tsabar kasala da sanyin gaɓɓai. Zuwa yanzu wannan fuskar bata aljani take fassarata ba, neman ƙarin bayani take a kanta a dalilin ganinta a waje biyu da basu da alaƙa da juna a zahirin rayuwa... Tajwar Eshaan da ke kishingiɗe bisa ƙayataccen kujera mai kama da wani madaidaicin gado gabansa butar shayi ce da ƙaramin kofin da alamu suka nuna yasha ko zai sha, idanunsa ya janye daga kan television da yake kallo ya ɗan waigo garesu. Akan Iffah dake tafiya tamkar hawainiya ya fara saukewa, fuskarta a sakaye take, hanunta dake riƙe da rigar jikinta ne ta ƙasa kawai a bayyane. Janye wa yay ya maida ga Malikat Haseenat. Ta ɗan hararesa da salon kulawa da nuna damuwa. Idanun ya janye a sannu daga kanta itama yana sakin kasaitaccen murmushi.... Harya gama gaisawa da kakar tasa a yanda yake kishingiɗe batare da ya motsa ba Iffah na tsaye ƙyam tamkar an dasata. Malikat Haseenat ta maida kallonta gareta tare da ambatar sunanta. A dake Iffah ta amsa dan tayi alƙawari ma kanta bazata taɓa barin rauninta sake bayyana ga kowa ba a yanzun. Kafinma Malikat ta sake cewa wani abu tai ƙasa a hankali, cikin rashin ƙwarin jiki ta zube ƙasan lallausan carpet ɗin da ko jikin zomo bazai nuna masa laushi ba. Ƙamshi ko ba'a magana dan ko'anan ake shukashi iyaka kenan. “Amincin ALLAH ya tabbata a gareka”. Ta faɗa badan har zuciyarta abinda take son faɗar kenan ba. Sai dai kwarjininsa daya mamaye falon da duk girmansa take jinta a matse yaƙi bata damar fitar jin zafinsa dake a ƙasan zuciyarta a zahiri. Kamar a waccan ranar yau ma bai amsa ba, babu ma alamar yajita tattare da shi. Daga cikin hular alkyabbar jikinta ta cije lips ɗinta da masifar ƙarfi tamkar zata hudasu da haƙori..... “Ai ma Zawjata-almilk rakkiya ɗakin da Tajwar zaiyi barci a yau”. Furucin Malikat Haseenat ga hadiman dake rakuɓe gefe zube a ƙasa kawunansu rissine tun shugowarsu ya nema sarƙe numfashin Iffah da Tajwar Eshaan a lokaci guda. Babu wanda Malikat Haseenat ta kalla a cikinsu sai ɗaya daga cikin Hadiman ce da suke girki ta miƙe da rawar jiki zuwa inda Iffah take. Dole ta mike dan a furucin Malikat Haseenat babu wasa ko ɗaukar turjiya ga kowannensu.... Shiru falon babu wanda ya sake ƙwaƙwƙwaran motsi har hadimar data raka Iffah iyakar ƙofar ɗakin ta dawo Malikat Haseenat ta sallamesu. Da ga shi sai ita suka rage, dan haka ya kafeta da idanunsa. Kai Malikat Haseenat ta ɗauke gefe tamkar bata gansa ba ko fahimtar kallon. “Anan zata zauna, sai ka zaɓi inda kake buƙatar ta kasance har tsahon sati ɗaya, dan zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu masu mata hidima zasu kasance tare da ita. Na damƙa amanarta a hannunka, ina kuma fatan ta kasance ƙarƙashin kariyar UBANGIJI. Fatan alkairi da shiga sabuwar rayuwa, tare da tayaka murnar sabon aure. Na barku cikin amincin ALLAH”. Da alama gushewar numfashi da rikicin wannan tsohuwa ya gama daskarar da jinin Shahan-shan. Dan harta fice a falon ko gashin idonsa bai ƙyafta ba, kai kace wani butun butumine aka dasa a wajen domin tarihi....... (🤔Tsohuwar nan kuwa na lafiya? Zata kai mana Iffah har ƙuryar Dodon Mayu🥱🤦). ★★... ★★.... Duk da dare ne gaba ɗaya masarautar ta ɗauki ɗumi bisa wannan bahagon hukunci na Malikat Haseenat. Basu da al'amarin yazoma a bazata ba, hatta Malikat Bushirat da Daneen Ammarah da Jasrah da akai zaman da su komai ya musu cak. Abinda suka sani kawai komawar Iffah sashenta, bawai kaita turakar Shahan-shan ba. Miyasa Malikat Haseenat ta canja lissafin a kan kansu suma?. Wannan itace tambayar daketa musu kaikawo su duka. “Ni kam dai a wannan gaɓar na kasa gane komai wlhy Akia. Shin minene dalilin Mamma nayin haka? Miyasa lissafin ya canja daga yanda muka tsara gaba ɗaya?”. Kamar malikat Bushirat bazata tanka har ta kai ta kawo kusan sau uku kafin ta dubi Jasrah mai maganar. “Kaina ya kulle Jasrah”. Ta faɗa a takaice da kaiwa zaune bakin gadon ta dafe kanta. “Ya ALLAH! Wlhy zuciyata ta fara kai ni ga hasashen wani abu daban?”. Jasrah ta sake faɗa tana dafe nata kan itama. ★ A ɓangaren Daneen Ammarah ma dai a rikicen take. Sai dai ita nata lissafin yasha banban da nasu Malikat Haseenat. Daga ɗakin taro bedroom ɗin Malikat Haseenat ta wuce zaman jiranta. A zaman da bai wuce mintuna arba'in ba kuwa sai gata. Kallo ɗaya taimata ta ɗauke kai. Hadimar dake biye da ita ta ajiye madarar hanunta da zubewa ƙasa tana gaida Daneen Ammarah. Hannu kawai ta ɗaga mata.... “Na matuƙar gajiya, kwanciya kawai nafi buƙata”. Malikat Haseenat ta faɗa tana wulla kekenta hanyar bathroom ɗinta batare data sake kallon Daneen Ammarah ba. Da kallo ta bita cikin shakku da shan jinin jiki. Dan duk da a dunƙule tai magana tana nufin bata bukatarta a ɗakin kenan. Jiki a sanyaye ta miƙe ta fice zuciyarta na faman tsalle-tsalle... Duk yanda taso kwanciya ta kasa hakan, fargaba da tausayin Iffah ne ke matukar ɗawainiya da ita. Har cikin zuciya bata son rasa yarinyar dan ta matuƙar shiga ranta. Soyayya take mata irin ta ƴa da uwa. Ita kanta har takanyi mamakin yanda takejin Iffah a rai matuƙa, amma tasan wannan ƙaunar daga ALLAH ne kawai. Wayar dake a hannunta ta ƙara rumtsewa, ta gwada kiran Iffah ya kai sau huɗu kenan amma tana fasawa, so take taji lafiyarta ko zata samu ƴar nutsuwa, amma wata zuciya na gargaɗarta da kalmar rashin dacewa.... ★★..... “Mi wannan tsohuwar ke nufi wai shin? Ko itace abin neman mu kamar yanda barbushi ya sanar mana?”. Miran Arshaan yaja numfashi ya fesar, kamar bazaice komai ba sai kuma ya kafe Miran Jasim da kallo yana girgiza kai. “Wlhy kaina ya kwance Jasim Akhi. Na kasa gane komai a wannan gaɓar, abinda na sani kawai shine mutuwar yarinyar nan a wannan gaɓar tamkar mutuwar cikar birinmu ce, dan na gama ɗora dukkan hope ɗinmu a kantane. Bai kamata ta mutu a yanzu ba har sai ta ƙarasa mana aikin da muka kwashi tsahon shekaru muna ginawa”. “Miye mafita?”. Cewar Miran Jasim a firgice, dan zantukan Arshaan ɗin kamar sun zaburar da shi ne abinda ke gabansu. Kai tsaye Miran Arshaan yace, “Ziyartar Barbushi a wannan daren, kafin waccan sankaran matar da ban san amfaninta a tafiyarmu ba tazo ta ishemu da tsarin banza”. “Hakan yayi mun, babu amfanin ɓata lokaci kaje kayi shiri”. Kai Miran Arshaan ya gyaɗa masa, tare da mikewa ya fice. Da banzan kallo Miran Jasim ya bisa, cikin ƙanƙance idanu da wani shu'umin murmushi a fuskarsa “Ba matar can bace kawai abin banza a cikinmu, har da kai Arshaan, daka gama mun amfani zan kawar da kai, dan ni kaɗai nake son mulkar daular ruman batare da ɗan uba ko ɗaya ba da zai zame min abokin gaba, nasan idan har na barka kaima zaka zamemin maƙiyi dan burinka wannan kujerar ne na sani shashasha”... (🥱Waɗan nan mutane dai to bara nayi shiru dai🤫) *_ZAWJATA-ALMILK_* Duk da akwai wani ɗan ɓurɓushin tsoro a ƙasan zuciyar Iffah ta matuƙar dakewa da addu'a ta shiga ɗakin bayan ta gama ƙarema bangon dogon corridor ɗin da suka biyo kallo, ta jinjina kai cikin jin matuƙar ƙuna da tausayin talakawan ƙasan ruman baki ɗaya. Tayi imanin akwai dubbunan mutane dake barci akan titi cikin yinwa da ƙishirwa da yawa. Amma abin mamaki yau ga bangon ɗakin barcin Shahan-shan yasha ado da zinari matsayin fenti, “Taya ma imani zai zauna a zuciyar mutanen nan har su ɗauka rai wani abun mai daraja?” ta faɗa a zahiri idanunta na cika da ƙwallar baƙin ciki da ƙara jin tsanar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed..........✍️ (😭Hikenan Iffahr mu an shigo ɗakin mutuwa😱🙆). Ko miye dalilin Malikat Haseenat na kai Iffah turakar Shahan-shan kai tsaye haka? Miye dalilinta na canja abinda suka tattauna da su Malikat Bushirat? Shin ko dai malikat Haseenat ce T....😱🤫🤭?. Yaya zata kasance tsakanin Iffah da Shahan-shan ne? Ta wani ɓangaren abinda ke kashe Zawjata-almilk kuna ganin zai ƙyale rayuwar Iffah a wannan dare kuwa?. Gadai wasu ɓoyayyun maƙiya na sake fitowa. Irinsu Miran Arshaan (mijin Jasrah kuma ƙani ga Tajwar Haysam) da Miran Jasim (shima ƙani ga Tajwar Haysam). Shin wacece wai matar nan da suketa a ambata batare da sunanta ba?. Hhhh tabbas yanzu ne wasan zai fara. Sai ku shirya ku sake shiri dan sai a yanzu ne muka kalmashe bakin shimfiɗar labarin dake cikin littafin DAUƊAR GORA... Wasan na asali yanzu ne filin yinsa ya kammala. Masoya sai mu antaya kawai😉🥱🏇🏇🏇🏇. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽 _𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_32_* ........Ni'imtaccen ƙamshin dake tashi a katafaren ɗakin ta zuƙa ta fesar da cigaba da bin komai daki-daki. Ɗaki kam ya cika a kirasa ɗaki ga masu arziƙin dake ɗaukar duniya gidan zama. Sai dai ta gama ayyanawa a ranta babu wani ƙyale-ƙyale da zatai sakacin da zai ruɗeta har ya dakatar mata da ƙudirinta data fara taka tsanin nasararsa a yau insha ALLAH. Ta saki kasaitaccen murmushi da ware hannayenta iskar na'urar ac ta busota tare da ƙamshi, idanunta ta lumshe ta buɗe tare da tsuke fuska. Cikin wani kakkausan sauti daya bambanta da nata na baya ta furta. “Yanzu ne za'a fara wasan na gaskiya. Dodon matsafa MATAN ƘWARAI bisa kanka!!”... (🥱 Iffahn mu irin wannan alwashi haka🤔 kinfa fara bani tsoro😱🏇). ★★... Tun wucewar Malikat Haseenat ya bar falon shima. Tsaye yake jikin windown ƙaramin falonsa na hutawa da babu mai shigarsa sai shi ɗaya tak da amintacen hadiminsa mai gyarasa. Dan a doka ma hatta matarsa bata da hurumin shiga wannan falon a tsari da ƙa'idar masarautar. Hasken daya ƙawata cikin masarautar ya bashi damar iya ganin abubuwan dake kusa daga inda yake, sai dai kuma a zahiri idanun nasa ne kawai ke kallon zuciyarsa sam ba'a nan take ba. Ya kwashe tsahon lokaci a wajen kafin ya warware hannayensa dake goye a bayansa ya furzar da numfashi. Ƙofar ɗakin barci ƙwaya ɗaya dake a falon ya nufa. Shima tsaf yake tamkar anan yake zaman din-din-din. A maimakon kwanciya anan ɗin ma zaune yakai cikin kujerar dake ajiye a gefe domin hutawa kawai. Tun agogon ɗakin na juya sakanni da mintuna har ya koma awanni yana zaune idanunsa lumshe, ya kwantar da bayansa a makarin kujerar dake ɗan juyawa a hankali. A kallon fuska baka isa gane yanayinsa ba balle ka samu damar masa fassara. Bugawar agogon ɗakin mai nuni da cikar ƙarfe biyu dai-dai ta sakashi buɗe idanunsa da ƙarancin hasken ɗakin ya hana damar iya tantance launinsu a yanzu. Agogon ya tsurama ido tamkar mai lissafa daƙiƙun da suka cigaba da motsawa..... A ɓangaren Iffah wannan lokaci na dai-dai da kai goshinta ƙasa domin yima UBANGIJI suduja a karo na babu adadi. Tun bayan kammala lissafe-lissafenta da ƙidaye-ƙidaye ta zanzare rigar jikinta, ƙaramin akwatinta ta buɗe babu alamar damuwa tattare da ita ta sauya kayanta zuwa abaya. Daga haka ta nufi bayi bakinta ƙunshe da tarin addu'oin da taketa yi tun shigowarta ɗakin. A karan farko data buɗe fanfo da nufin yin alwala saɓanin zubar ruwa sai taci karo da jan abu tamkar jini. Tabbas taji firgici, amma sai tai yaƙi da rauninta wajen cigaba da addu'a da son daidaita harbawar da zuciyarta keyi da sauri-sauri. Tamkar almara kalar jan ya ɓace a idanunta ainahin ruwa ya maye gurbinsa. Numfashi taja ta fesar zuciyarta na tabbatar mata ta ƙara dakewa. Tsaf ta ɗaura alwalarta kuwa ta miƙe, tana ƙoƙarin gyara ɗan kwalinta taji tamkar an gitta ta bayanta. Anan ɗinma dai zuciyarta ta tsinke, amma sai ta cigaba da ambaton sunan ALLAH ta basar. Bata damu da nan wanin abin salla ba, dan tsaftar dardumar da aka ƙawata ɗakin da ita ya gamsar da ita. Mayafinta ta naɗa tai nagartacciyar tsayuwar salla domin fuskantar UBANGIJIN talikai mai jin kukan wanda ma basu fara kukan ba, mai bada kariya ga wanda ya yarda babu abin dogaro sama da shi... Taja tsahon lokaci a sujidar tana mai zubda hawaye da ƙaskantar da kai ga mai gani a duk inda ka ɓuya. Bayan ta sallame tai zaman karatun Alkur'ani a cikin wayarta dan batajin zata samu Alkur'ani a wannan ɗakin da ƙyaleƙyalen cikinsa ya tabbatar mata zamowa fadar aljanu ba komai bane. Sai da ta gama karance baƙara har zuwa inda suka tsaya a makaranta sannan tai addu'a mai tsawo itama. Sosai taji wata iriyar nutsuwa na ratsa dukkan jikinta, ta sauke ajiyar zuciya da miƙewa. Hankalinta kwance ta haye katafaren lafiyayyen gadon da Shahan-shan ne kawai ya taɓa hawansa a tarihi. Nanma zama tai tai addu'ar barci ya shafe jikinta ta gyara lausasan filos ɗin da aka ƙawata adon gadon da su ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya. Barci mai daɗi ya fara fisgar idanunta a sannu-sannu sai gata tana sauke numfashi....... ★★...... ★★..... ★★....... Bayan wucewar saurayin da Kaka ya shimfiɗama sha tara na arziƙi gidan yay shiru. Kamar yanda bai cema Iyyani komai ba itama batace ba, tsahon wasu mintuna sannan ya miƙe ya shiga ɗakinsa. Tashi Iyyani tai ta bisa, dan ta fahimci maganarce baya buƙatar ayi sam.. A ɗakin ma baice mata komai ba har tsahon wani lokaci, ganin haka ta katse shirun da faɗin, “A haɗa maka ruwan wanka?”. Batare da ya bar abinda yake ba ya jinjina mata kai. Fita tai jiki a sanyaye, babu jimawa ta koma ta sanar masa an haɗa. “ALLAH yay miki albarka”. Ya faɗa kamar yanda ya saba. Ta ɗan ji sanyi a ranta, dan haka ta amsa da “Amin tare da kai” cikin sauke ajiyar zuciya.... “Ai bakaci wani abincin kirki ba”. Iyyani ta faɗa idonta akan kwanikan gaban Kaka da ya gama cin abincin data kawo masa bayan fitowarsa wanka. Kai ya jinjina mata da sakin murmushi a karan farko tun bayan shigowarsa gidan. “Alhamdulillahi wanda naci ya wadatar dani”. Kai kawai ta jinjina masa jikinta na ƙara sanyaya. Duk wanda zai sam mijinta a bayanta yake, ta san murmushin sa ba yana nufin farin ciki bane na tsantsar damuwa ce..... “Yaya jikinta?”. Ya katse tunaninta da abinda taketa zumuɗin san ji a bakinsa. “Alhamdulillahi da sauƙi”. “ALLAH ya ƙara afuwa. Bara na ganta”. Ummu na zaune shiru ta tsurama waje ɗaya idanu suka shiga. Har suka kai zaune gefenta babu alamar tana san da zuwan nasu. Kaka ya kafa mata idanu na wasu sakanni sai kuma ya kauda kai. Taɓata Iyyani tayi, ta kawo nannauyan numfashi da ɗan zabura na ganinsu a ɗakin dan da gaske bata san da shigowar tasu ba. Kaka ta kalla idanunta na cikowa da ƙwalla, sai kuma ta duƙar da kai ta fara gaishesa. A hankali ya nisa kafin ya amsa a taƙaice kamar yanda tai gaisuwar. “Jumaimah!”. Ya kira ainahin sunanta. “Na'am Baba”. Ta amsa akan laɓɓanta. “Damuwa ko ƙuntata kai bata sauya ƙaddarar bawa. Juriya da tsantsar jarumta baya hana ƙaddarar zuwa. Haƙilo ko nuna ƙarfin iko baya ture ta a lokacin da aka so. Rauni ko rashin tawwakali bazai dawo maka da abinda dama can ba naka bane ba. Haƙuri shike samar da komai koda kuwa a zahiri yafi ƙarfin ƙarfinka”. “Hakane Baba”. Ta faɗa cikin rawar murya. Murmushi ya saki da matsawa kusa da ita sosai. Ɗa a gaban iyayensa baya girma koda ace yayi furfura a saman kai. Kaka ya riƙo hanun Ummu cikin nasa, ɗayan kuma ya shafa kanta. “ALLAH yayi miki albarka. Yasa ƙaddarar su ta zama kaffara a garemu baki ɗaya.” “Baba mun rasa su suma ko?”. Ummu dake dubansa idanu cike da ƙwalla ta faɗa. Murmushin ya sake sakar mata. Sai kuma ya girgiza kansa da kwanto da kanta bisa kafaɗarsa. “Bamu rasa su ba, ba kuma mu fidda rai da samunsu ba”. A hankali hawayen da suka kasa fita a idonta tsahon kwanaki suka fara sauka a kafaɗarsa....... ★★.... ★★.... ★★..... Mummunan mafarkin da ALLAH ya bata ikon cin galaba a cikinsa ta farka a zabure, cikin amincin UBANGIJI harshenta ya ambato addu'ar tashi daga barci kamar yanda musulinci ya ɗoramu akai. Ajiyar zuciya ta sauke da saka gefen bargon data lulluɓa ta yarce gumin da yay ma goshinta jalab, sai kuma ta sake lumshe idanu jin sautin kiran salla da take ƙyautata zaton a masallacin cikin masarautar ne. Hasken ɗakin ta kai hannu ta ƙara, ta bi ko'ina na cikinsa da kallo tamkar zataga munanan halittun data gani a cikinsa a mafarki. Rashin ganin komai a zahiri ya bata ƙarin gwiwar sakkowa a gadon ta nufi toilet. Bata damu da rashin ganin Tajwar Eshaan a ɗakin ba duk da taji Malikat Haseenat ta ambata nan ɗin matsayin ɗakin barcinsa na daren jiya. Ƙarancin shekarunta da wautarta yasa bata ɗauki tsallakewar komai ba. Abinda kawai zuciyarta ke mata kaikawo a rai shine ta tsallake daren na jiya dai koma yaya ne, ta tsallake tarihin mutuwa a daren kwana turakar dodon matsafa. Dalilin tsallakewar, ko barinta da yay da ranta ne bata sani ba, ba kuma tasan tayaya ya kamata ta sani ba. Abinda kawai take da damar yi shine buɗe kunne da idanuwa taga mizai biyo baya ga kowa da kowa. A yanzu ɗin ma tayi zaton ganin jinin kamar jiya dai, sai dai babu alamar hakan har ta kammala uzirinta tayo alwala ta fito. Tana idar da salla wani irin nannauyan barci ya dinga fisgar idanunta. Dakewa tai cikin dauriya tai zaman yin azkar, da ƙyar ta iya kammalawa barci yay mata baban fisga a wajen dole takai kwance tana ambaton sunan ALLAH. A hankali ta fara sauke numfashi alamar barcin nata mai nauyi ne.... ★★.... ★★..... A cikin masarauta tako ina an gama baza kunnuwan jin fito da gawar Zawjata-almilk. Hatta da Malikat Haseena bata tare da nutsuwarta gaba ɗaya. Tun ana ƙirga sakanni a bayan sallar asubahi har aka koma mintuna, mintuna suka koma awanni babu wani labari. A take aka koma ƴar ƙus-ƙus tun daga kan hadimai har manyan masu faɗa ajin masarautar. Yayinda suma Hadiman sashen Shahan-shan suke zaune jigum-jigum na jiran tsumayen abinda kowa keda tabbacin zai kasance. bakunansu cike yake taf da abubuwan faɗa akan abinda suka wayi gari da shi mai matuƙar rikitarwa da zai maimaita faruwa bayan ya faru ga duk wata Zawjata-almilk data kwana ta tashi a wannan sashen. Duk ɗunbin yawan abin cewar iyakarsa zukatansu dan ko'a tsakaninsu bai faɗuwa balle gulmantawa a waje saboda tako ina camara ce zagaye da su..... *_★MALIKAT BUSHIRAT★_* Ba'a safiyar yau ba, ita tun ma a daren jiya tai hanun riga da nutsuwa. Gaba ɗaya a daren ko sau ɗaya bata iya ta rintsa ba. A maimakon barci ma idanunta akan sashen Shahan-shan da kowa ke iya gani daga nasa sashen a cikin masarautar suka kwashe mafi yawan awannin daren na jiya. Tayi yunƙurin kiransa amma wayar a kashe, hakanne ya sake ɗaga mata hankali da jin zafin wannan hukunci na Malikat Haseenat a karo na farko. A ganinta ganganci ne miƙa nagartacciyar yariya irin Iffah hannun gudan jinin nata bayan Mamma tasan minene makomar yin hakan ga rayuwar yarinyar. Duk jarumtarta a duk sanda ta tuna zuwa safiya gawar yarinyar ce zata fito takanji ƙwalla sun cika idonta. Amma takan danne ta hanasu fitowa har garin ALLAH ya kammala wayewa... Tun idar da sallar asubahi bata iya ta motsa ba, ƙirjinta ne ke matuƙar bugawa da jiran tsammanin mummunan labari..... *_★DANEEN AMMARAH★_* A ɓangaren Daneen Ammarah itama a kwatankwacin irin halin da Malikat Bushirat ta kwana ta tashi take ciki. Dan ita kwana tayi ma tana hawaye. Har ƙarƙashin zuciya takejin matsanancin ƙaunar Iffah. Tana jin yarinyar a matsayin cikon wani gurbi data rasa irin na kowace uwa mai shekarunta. Sai gashi Mamma da ta fara bata tsoro a daren jiya ta rusashi da maye gurbinsa da fargaba mai matuƙar tsanani da razani. Wani mutum saɓanin jininta bai taɓa mamaye zuciyarta da ƙauna mai ƙarfin haka ba kamar yanda yarinyar tayi mata. Sosai take jinta a rai da jinin jikinta. Itama dai tun daga sallar asuba bata sake iya kataɓus ba tai zaman jiran tsammani irin na duk wanda ya kwana ya tashi a cikin masarautar....... ★★... ★★.... ★★.... Harya gota ɗakin cikin shiga ta blue ɗin jallabiya mai tsananin ƙyau da ƙyalli mai ɗaukar ido da nuna taushinta a zahiri dake nuna daga masallaci yake ya tsaya cak. Kamar bazai motsa ba sai kuma ya juya kansa a sannu yana kallon ɗakin. Kallon kusan minti ɗaya da wasu sakanni ya motsa gaɓɓansa cikin takunsa na izza da kame kai ya tura kai ciki. Da farko rashin lura da ita ya sakashi yin tsamm, sai dai fuskarsa ta nuna dakewa kamar koyaushe. Ya ɗaga ƙafa da niyyar juyawa ya fita idanunsa suka sauka a kanta. Yay tsai yana kallonta na tsahon mintuna kusan huɗu tamkar mai rarrabe ita ɗin ce ko wata? Dan a kallo ɗaya zaka fahimci salla ta idar a wajen barci yay awon gaba da ita. Ya ɗan furzar da numfashi da kauda kansa gefe ya sake bin ɗakin da kallo kai kace baƙonsa ne har ya sake direwa akan fuskar Iffah dake ta barcinta numfashinta na fita a hankali.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_33_* .........Ƙarfe takwas da rabi dai-dai agogon ƙasar ɗaya daga cikin amintattun Hadiman dake gyara ɗakunan barcin na Tajwar ta iso cikin faɗuwar gaba hanunta ɗauke da akwati da aka kawo yanzun nan daga sashen Malikat Haseenat matsayin kayan da Iffah zatai amfani da shi. Zuciyarta har wani zallo take na fargabar abinda take da tabbacin tozali da shi kamar yanda sukayi a baya ga sauran Zawjata-almilk da suka shuɗe. Ta tura ƙofar cikin sanɗa tana mai ambaton sallama da rawar harshe badan tana tunanin samun amsa ba. Ganin Iffah kwance a saman gado, lulluɓe da lallausan bargo baisa taji ƙwarin gwiwa ba. Tai yunƙurin ajiye akwatin hanunta, cak ta tsaya dukkanin idanunta na fitowa waje dan firgici ko sumar tsaye sakamakon juyi da Iffah tai alamar gyara kwanciya. Akwatin ta saki ƙasa ta shiga jan jikinta dake ɓari baya-baya harta dangane da ƙofa gab..... Iffah dake ƙoƙarin gyara bargo idanunta rufe ta buɗesu da sauri saboda jin ƙarar bigewar hadimar. Da mamakin jinta kamar a gado ya sata shashshafa hannunta. (Tabbas gadonne) ta ayyana a zuciyarta tana sake buɗe idanunta da ƙyau tana mai yunƙurin tashi zaune. Tuni hadimar nan ta sake firgicewa, da lalube ta murɗa handle ɗin ƙofar ta fita a guje. Kallon ƙofar Iffah tayi, sai dai hadimar ta gama ficewa bayanta kawai ta ɗan gani kaɗan da wulgawar mayafinta. da sauri ta yaye bargon da bata san ya akai yazo jikinta ba. Ta dire ƙasa mamakin duniya na cigaba da dabaibaye ta. “Wacece wadda ta fita? Mi tazo yi? Wai ta yaya ma na dawo saman gadon nan bayan a ƙasa na kwanta?”. Ta shiga jerama kanta tambayoyin da bata san inda zata samu amsarsu ba. Sai kuma ta ɗan kamo rigar jikinta ta kai hancinta. “Ya ALLAH, da gaske fa wannan mayataccen ƙamshin a jikina ne?”. Ta sake faɗa a fili tana sake shinshinar rigar...... A ɓangaren jama'ar masarauta dake a zaman jigum-jigum kam fitar hadimar nan ya isar da saƙon Zawjata-almilk na raye. Da farko duk wanda zancen yaje kunensa ɗaukewar numfashi na wucin gadi ne ke riskarsa, sai kuma rashin gaskatawa a zahiri ya biyo baya. Hatta da Malikat Bushirat da Daneen Ammarah yanayi da ruɗanin jin hakan bai tsallakesu ba suma. A kusan tare suka ɗauka wayoyinsu domin neman Iffah ko zasu samu jin gaskiyar zance. Cikin Sa'a kuwa ta Daneen Ammarah ta fara shiga.... Iffah na zaune har yanzu cikin ɗaurewar kai akan wanda ya maidata saman gado da wulƙawar fitar wadda bata sani ba wayarta ta katseta. Numfashi taja ta fesar da ɗan ƙarfi tana kai hannu akan wayar. *_Mamy_* ta gani rubuce ɓaro-ɓaro. Ganin zata katse tai ƙarfin halin ɗagawa ta kai kunne tana faɗin, “Assalamu alaikum. Amincin UBANGIJI da rahamar sa su yalwatu a gareki Mamy barka da safiya”. A matuƙar razani da motsuwar zuciya Daneen Ammarah taja numfashin dake neman ƙwace mata. “Ibnati!”. Ta ambata cikin son tabbatarwa. “Na'am Mamy”. Iffah ta amsa kanta tsaye babu alamar irin fargabar dake harshen Daneen Ammarah ɗin a tattare da ita. Dan ita wanda ya ɗauketa daga ƙasa ya maida saman gado da fitar macen data ganine kawai damuwarta a yanzu. Daneen Ammarah da taji al'amarin tamkar a mafarki ta lumshe ido hawaye na silalo mata saman ƙyakykywar fuskarta a hankali. Ƙasa takai durƙushe tana mai godema UBANGIJI ta hayar kai goshinta ƙasa tai sujjadar shukur... Iffah da mamaki ta cigaba da ambaton “Hallo Mamy! Mamy kina jina kuwa?”. Shiru babu alamar za'a amsa. Yanke wayar tai da yunƙurin sake kira a zatonta matsalar network ce sai ga kiran Malikat Bushirat ya shigo shima. Ɗan jimm tai tana kallon wayar, sai kuma ta ɗaga takai kunne da sallama nan ma. Malikat Bushirat da idanunta ke cikowa da ƙwalla sakamakon jin muryar Iffah tar-tar a kunenta ta kai zaune tana ambaton sunan ALLAH. Iffah na son tambaya tana jin nauyi, sai kawai tai shiru tana sauraren kalmomin godiya ga ALLAH da Malikat Bushirat ɗin ke ambata daga can. (Ya rabbi! Wai mike faruwa ne haka?) Ta ayyana a zuciyarta da al'ajabi. Knocking ƙofa da akai ta hanyar danna alerm a dai-dai lokacin ya katse tunanin nata. Ta kai dubanta ga kofar babu alamar zata tanka har aka sake danna alerm ɗin sannan tai ƙarfin halin amsawa da bada umarnin shigowa tana gyara mayafin data yanama kanta.. Hadimar ɗazun ce dai ta shigo ɗauke da ƙaramin tray mai ɗauke da butar shayi. Kanta a ƙasa ta ajiye a inda ya dace tana mai zubewa ƙasa durkushe. “Amincin ALLAH da tsahon rai mai albarka su kasance tare da Zawjata-almilk Barka da safiya”. Iffah da ke kallonta ta amsa cikin motsa lips ɗinta kaɗan. Sabo da hakan yasa hadimar bata damu da rashin amsawar Iffah ba. Cikin sake rissinar da kai tace, “Ya Zawjata-almilk yanzu lokacin wankanki ne, bayan nan karin kummalo na jiranki tare da Shugabana”. Yanzu ɗin ma kamar Iffah bazata amsa ba sai kuma ta jinjina kanta. “Kije abinki zan fito”. “Umarninki shine abin jirana. Amma a gafarceni zan haɗa ruwan”. “Kije abinki zan yi komai da kaina”. Babu yanda hafimar ta iya dole ta miƙe domin bin umarni shine kawai huruminsu. Da kallo iffah ta bita abubuwa masu yawan gaske na son fara mata kutse a ƙwaƙwalwa da zuciya. Ƙwarin gwiwar da take bama kanta akan turesu ya sata miƙewa ta nufin toilet tana mai ambaton addu'ai a bakinta saboda tuna abinda taci karo da shi a daren jiya a toilet ɗin. Ko'ina tsaf, kuma cikin ƙamshi irin na daren jiya. Sai da ta ƙarema komai kallo fiye da jiya kafin ta ɗage kafaɗa irin na koma miye ta shirya masa. Tsabagen rigima da wuce wuri ko tsageranci za'ace ta haɗa ruwanta mai ɗumi da zuba duk wani nau'in turaren wanka da aka jera domin Shahan-shan ta shige cikin kwamin wankan tai luf. Sai da taji ko'ina nata ya miƙe yanda take buƙata sannan ta fita a ruwan domin fara wanka... Tsaf ta kammala shirinta cikin doguwar rigar material sky blue da akaima ɗinkin daya fidda ainahin halittarta tamkar ƴar tsanar roba. Rigar ta zauna mata ɗas, siririn mayafin da aka haɗa rigar da shi ta naɗa tamkar yanda larabawa keyi, ta ɗakko after dress shara-shara mai kamar alƙyabba ta ɗora a sama kalar blue sosai. Ta ɗanji babu daɗi na rashin turarurrukanta tare da ita, dan ko waɗan nan kayan ganinsu kawai tai, cikin ɗan taɓe baki da ɗage kafaɗa a zahiri ta dinga kwasar turarrukan da taci karo da su a ɗakin cikin wani ƙyaƙykyawan glass dake kusa da mirror ta dinga zazzagama jikinta har sai da ta gamsu ƙarfin kamshin zai kai duk inda mai rai ke numfashi a sashen sannan ta haƙura. Idanunta ƙyam a mirrorn ta saki ƙayataccen murmushi da kanne ido ɗaya a fili ta furta “Irin wannan haɗuwa haka autar Ummu”. Tai salute ɗin kanta.... Sautin ƙarar takun takalman ƙafarta da mayataccen ƙamshin tiraren da shi kaɗai aka sani da shi ya sashi tsayawa cak daga ƙoƙarin kai hannu a abincin da aka gama haɗawa gabansa. Fararen idanunsa tar-tar tamkar madara ya ɗago ya sauke a kanta. Hakama hadiman dake a tsaye ta gefe da gefensa kawunansu a ƙasa cikin yanayin mutuwar tsaye data rikesu suka zube ƙasa kan gwiyawunsu illahirin jikkunansu na ƙyarma akan dalilai guda biyu. Na farko ganin tabbatar da wadda suka gama fidda rai da jiran tsammanin ganin an shigo fidda gawarta tamkar Zawjata-almilk na baya dai na raye ɗin kamar yanda Hadimar ta gano. Na biyu ƙamshin turaren jikinta da ga mutum ɗaya tak ake iya jinsa a duk faɗin ƙasar ruman ma bawai a daular ruman ba... Tamkar Iffah bata fahimci halin da suke a ciki ba ta ƙaraso cikin katafaren falon batare data dubi ko ɗaya a cikinsu ba balle mai gayya mai aikin. Cikin sauri ɗaya daga cikin hadiman ya miƙe ya gyara mata kujera, zaune ta kai tana mai dubansa a karo na farko. Tuni shi kuma ya maida kansa ga abinda yake yi tamkar bai san da zuwan tan ba. Ta taɓe baki da juya idanunta ta maida ga hadimar dake ƙoƙarin fara haɗa mata abincin. Nunin abinda take buƙata tai mata da ɗan yatsa. Hadimar na kammalawa ta koma cikin ƴan uwanta ta tsaya itama kanta a rirrine. Gaba ɗaya jinta take a takure, kwarjininsa ya cika ko'ina a falon. Cikin dakewa da kaucewa gizago sa ta ɗan ɗago ta ɗan saci kallonsa da nufin gaishesa idanunta suka shige cikin nasa da ya ɗago da nufin kallon nata... “Who are you?” Ya fara faɗa cikin basarwa yana kaɗa idanusa da har yanzu ke cikin nata tamkar bashi yay maganar ba. Badan a idanunta tausasan lips ɗinsa suka motsa wajen ambaton wacece itan ba zata iya gaddamar hakan. Kaifin idanunsa sun neman sage duk wani ƙwarin gwiwarta. Ƙoƙarin fara sassauta nata idanun tai yunƙurin yi cikin ƙanƙance su sannu a hankali. Shima sai ya kankance nasa kamar yanda takeyi, fuskarsa na sake tsukewa babu alamar sassauci tattare da ita. Nata ta fisga da ƙarfi ta lumshe su, sai kuma ta buɗe a kansa tana mai sake tsuke tata fuskar itama, bazata iya jure salon nasa ba dake neman ƙone ƙudirinta, dan haka ta kauda kanta gefe babu alamar zata bashi amsar da yay yunƙurin ji daga garetan.. “Barka da safiya”. Ta faɗa a ƙoƙarinta na basar da tambayarsa ta farko. Bai motsa ba, babu alamar kuma zai amsa ta. Hakan sai ya sake sukar zuciyarta harta ɗan saci kallonsa, da sauri ta kauda idanunta, dan da gaske fuskarsa ruguza mata lissafi take, da gasken gaske shi ƙyaƙyƙyawa ne, irin ƙyawun dako a cikin ƙasar tasu ake yabawa da shi, koda yake batai mamakin hakan ba, dan Malikat Bushirat ba'a magana, duk da girma ya fara zuwa gareta tsantsar ƙyawunta a bayyane yake. Hakama Malikat Haseena dake matsayin kakarsa data haifi babansa tunda ita dai bataga baban nasaba ko'a hoto har yanzun, amma zubin Malikat Haseena dana Daneen Ammarah ya tabbatar mata shima ɗin dai zai kasance ƙyaƙyƙywan ne...... “What is your goal in life?”. Kalmomi guda shida suka katse mata tunani a bazata. Ta kallesa tana ƙoƙarin danne mamakinta kan waɗan nan tambayoyi da yake faman yanko mata kai tsaye. Ganin yanda ya zuba mata ƙasaitattun idanunsa masu firgita mara gaskiya ta janye nata tana yamutse fuska. (Damarki ce wannan) wata zuciya ta ayyana mata. Cike da gamsuwa ta sake kauda kai gefe dan har yanzu tanajin kaifin idanunsa a kanta. “Ni ban kasance kowa ba sai talakar dake a ƙarƙashin mulkinka ranka ya daɗe. Abinda nake son cimmawa kuwa a rayuwata irin abinda shugaba ke fatan cimmawa ga talakawan ƙasarsa ta hanyar mulkarsu da fuska biyu ne”. Yanda tai maganar kanta tsaye babu ko ɗar ya sashi jin mamakinta. (Tabbas wannan abar ba mutum bace) zuciyarsa ta tabbatar masa. A zahiri sai ya ɗauke kansa cike da basarwa. Shiru babu alamar zai sake tankawa har Iffah tama fidda rai ta cigaba da tsakurar abincinta kamar yanda yakeyi shima. “Wasa da rayuwarki kuskurene ga ƙarfin halinki, ƙin kasancewar ki tarihi a wannan safiyar bashi ke tabbatar miki nasarar tsallakewa ba”. A yanzun kam zantukansa sun zama masu matuƙar tasiri a fitarsu da saurarensu gareta, jin bazata iya dannewa ba ta amsa batare data ɗago ta kallesa ba, “Hakane shugabana, sai dai fa _Fate is some thing undeniable”_ Ya basar babu alamar yanzu ma zai amsa, shayin sa ya kai baki cike da ƙasaita. Itama sai bata sake cewa komai ba ta cigaba da cin abincin tana mai kallonsa ta gefen ido, sannu-sannu tabi sautin motsa plate ɗin gabansa da kallo har kan lallausan farar fatan hanunsa masu ɗauke da tsaftatattun fararen dogayen farce, baya tai ƙoƙarin jan jikinta batare data yarda idanunta sun wuce kallon hanun nasa ba. Yanda ya basar da ita ɗin kuma sai yay matuƙar sukar zuciyarta, dan bata buƙatar tattaunawar tasu ta tsaya iya haka. Amma sai bata yarda fuskarta ta nunaba. Sai ma mamakin ƙasaita da tsantsar izzar wannan bawa da zuciyarta ke faman yi. A wani ɓangaren ita kanta dakewa kawai take, amma kwarjininsa da gizago na firgita ta matuƙa. Tana ƙara tsarkake sunan ALLAH akan yarda da jinin mulki gaskiya ne. Duk da ta shigo daular ruman da wani ƙudiri a ranta hakan bazai hanata girmamashi ba, koda ace tayima yunƙurin hakan kwarjinsa bazai bata damar yin saɓanin girmamawar da kowa ke masan ba. So take taji tsanarsa a ranta kamar yanda takeji kafin ganin wannan fuskar matsayin shi amma zuciyarta taƙi bata haɗin kai. Numfashi taja a hankali ta fesar a ƙasan maƙoshinta. “Kokawa da ƙaddara a fuskar iyawa na nufin faɗuwa! Kinga ko what you get is, what you have?”. Ya faɗa cikin katse mata tunani dai-dai yana ɗagowa.......✍️ “Fareedatu kibar danginmu su tsinkayi yini da kwana cikin sallama, Banda taro dutsen zuma inake ina kace nace da dodon may...🥱🏇”. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_34_* ........(Mi wannan mutumin ke ƙullawa?). Ta faɗa a zuciya batare data motsa ba. (Keda ke neman kusanci da shi dama miye matsalarki da koma mi yake nufi) wata zuciyarta ta sake ayyana mata. tamkar wadda aka zaburar sunan Arfa da Fariha ya fara amsa kuwwa a zuciyarta har tana jinsa yana tashi bisa sararin samaniya. Kaifafan idanunsa masu nuna tsaurinsa ya zuba mata ganin ta basar da shi itama. Kusan mintuna uku babu alamar zata tankama zancen nasa har ya fara jin haushi. Ta taɓe baki da kauda kanta gefe, cike da dakewa ta furta, “Da gizago na tsorata ƙwarin gwiwata da bazan amincewa shigowa ramin zakin da ɗanyen nama shine abincinsa ba. Karka damu a kaina ranka ya daɗe, dan a wannan gaɓar *_cuta ce ta ɗakko cuta, ɓarawo ya ɗakko akwatin maciji”._* Fuska ya ɗan motsa kamar zaiyi murmushi, sai kuma ya basar. “Bana haɗa ƙwanji da mage duk da kamaninta na yanayi da nawa matsayina na ZAKI har a hallaya. Ki kama kanki dan kina buƙatar rayuwa mai tsaho wajen moran ƙuruciyarki”. Ya faɗa da muryarsa mai zurfi da ƙasaita yana miƙewa ya zagayeta ya wuce abinsa. Shiru bata motsa ba har ta gama jin ɓacewar sautin takunsa a wajen, ta ɗan cije bakinta “Zaki zako ka magantu fiye da haka”. Ta faɗa a fili cike da kwaikwayo salon maganarsa tana sakin wani lallausan murmushi da kai kofin shayi a bakinta, duk da zafinsa ta rumtse ido ta kwankwaɗe abinta sannan ta juya taima hadiman dake tsaye har yanzu kallo ɗaya ta ɗauke kanta batare da damuwar komai ba, dan tasan basuji komai ɗin ba da suka tattauna. A yanda suke maganar ma wani sai ya ɗauka wani zancen soyayya ne ya haɗasu. Komai batacema kowa ba itama ta miƙe tabar wajen, duk suka bita da kallon ƙasan ido kowa da abinda yake ayyanawa a zuciyarsa. A tafiyar tata tana ɗan kalle-kalle taci karo da camara, komai bataji a ranta ba, dan tayi tsammanin hakan tun farko, saboda babu yanda za'ai sashen mutum mai ƙarfin iko kamar Tajwar ace babu wani tsaro makamancin hakan koma fiye da hakan. Da ƙyar ta iya gane ɗakin data kwana. Tana shiga ta zube a kujera da sauke nauyayan numfashi, ɗakin da akaima gyara ɗan gaske tabi da idanu, sai taga ma kamar ba'a cikinsa ta kwana ba, ganin akwatin kayanta kawai ya tabbatar mata da shi ɗin ne. Tunani mai ƙarfin gaske ta faɗa kusan kashi uku zuwa huɗu musamman akan kawota da Malikat Haseena tayi, mi tsohuwar ke nufi da haka bayan su suka sanar mata an rasa matan baya ne a dalilin kawosu turakar Shahan-shan ɗin. Sai kuma akan Tajwar Eshaan ɗin, na farko waccan fuskar data gani a waje kafin shigowarta masarautar matsayin matarsa. Na biyu wannan fuskar ta yanzu da bata da banbanci da waccan ɗin, na uku hanyar da ya kamata ta cigaba da bi domin sanin ainahin wanene Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed a baɗini da zahirin rayuwa. Domin da gasken gaske tana a cikin ruɗani akan fuskokin nan biyu data gani a mabanbanta muhallai. Su ƴan biyu ne? Kokuwa shi ɗinne ke ɓadda kama yana fita?. Abu na uku kuma abinda ya faru a daren jiya da sai a yanzu yake bata matuƙar mamaki, tun a jiyan bawai ta ajiyesa a gefe bane dan bashi da muhimmanci ga haɗarin da tasan ta kawo kanta ciki, kawai dai bata san dalilin da yasa bataji ko ɗar ba a zuciyarta na tsoro, kuma har yanzu batajin tsoron sam, dama kuma tun asali bata da tsoron. Dan Iffah irin mutanen nan ne masu ƙesashiyar zuciya mai iya tunkarar komai koda yanada haɗari a garesu, tanada naci da zama kaifi ɗaya akan zimma da cimma buri duk da ƙarancin shekarunta. Na ƙarshe tattaunawarsu ta yanzu da shi da girman kalaman da yay amfani wajen jifanta da su. Ta ɗan murmusa da cije lips ɗinta tana mai lumshe idanu a hankali...... ★★.... ★★..... Zuwa yanzu tako ina maganar tsallakewar Iffah ce ke kaikawo a cikin masarautar. Kowa ya nutsu wajen tattauna abinda ke bakinsa da abokin maganarsa. Wasu jin daɗine game da hakan, wasu ko baƙin cikine a ransu, dan mutuwar Zawjata-almilk ɗin kamar wani makamine a hannayensu na dukan nasarar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ɗin. Tsallakewar Iffah kuma zai kasance kamar damar ƙalubalantarsa da suka riƙe ya kuɓuce musu kenan. Ita kuma yarinyar kimarta da nunawa duniya tafi ƙarfin masu ƙarfin zai yi tasiri a zukatan jama'a..... ★Komai dake faruwa yana isa da shiga a kunnen manyan masu faɗa aji ta bangaren iko da kusanci da Tajwar Eshaan ɗin. Wato Malikat Haseenat da Malikat Bushirat. Sai dai sunyi biris babu alamar zasu tofa nasu akan hakan bayan bayyanar farin cikinsu akan fuskokinsu daya gaza boyuwa ga kowa. Dan a dalilin wannan al'amari Malikat Bushirat har ƴafiya tayi ga wasu firsinoni dake a cikin kurkukun masarautar akan wasu laifuka nasu da basu kai sun kawo ba. A cikin sunne kuma aka sallami harda Diwa a dalilin bincike daya tabbatar da bata da hannu game da abinda ya faru ga Iffah a waccan ranar. ★A ɓangaren Malikat Haseenat kuwa maimakon bama abinda ke zuwama kunenta muhimmanci hankalinta ta maida wajen tantance hadiman da zasu koma aiki a karkashin Iffah ne bisa taimakon Daneen Ammarah da farin cikinta itama yake a bayyane. Dan itama dai har kyaututtuka na musamman yau ta bada ga hadimai tare da sakawa a tattaro mata dukkan malaman masarautar zuwa sashen Iffah da bukatar suyi saukar Alkur'ani mai girma. Ta kuma miƙe da karfin jikinta wajen shirya lunch na musamman ga Tajwar Eshaan da amarya Iffah Zawjata-almilk... *_★BARRISTER★_* Abubuwan da suka faru sun sakashi dakatawa a zahirance bisa shawarar Kaka. Sai dai yana cigaba da gudanar da wani binciken sirri dan yayma kansa alƙawarin binciko duk mai hannu akan wannan al'amarin nasu Babiy da ma inda aka ɓoye su. Kamar yau ma tun jijjifin safiya ya fito daga gida. Kai tsaye hanyar jihar Hubab ya nufa inda bincikensa ya tabbatar masa nanne ainahin jihar da matar Abu Moosa ta fito. Jihar Hubab makwafciyar Dahab city ce (Daular ruman kenan) dan haka a cikin ƙanƙanin lokaci ya isa. Bai tsaya sanyaba ya ɗauka hanyar ainahin kauyensu kuma. Kasancewar anan ma hanyace shimfidaɗɗiya a kanƙanin lokaci ya isa. Da farko ya sha wahalar binciken inda gidansu yake, sai da yay dabarar nuna hotonta sannan. Kusan mintuna goma bayan isar da saƙon tanada baƙo gareta ta fito cikin irin shigarsu. Tayi ɗan tsamm alamar shan jinin jikinta kafin ta ƙaraso a yanayin son basarwa. Barrister shi ya fara gaidata, tare da sanar mata sunansa. Lokaci ɗaya ruɗani ya bayyana akan fuskarta ta shiga waige-waige irin na rashin gaskiya da ƙoƙarin ja baya daga garesa... “Bawan ALLAH ina baka shawara ka taimaki kanka ka bar ƙauyen nan, babu wani abu da zaka iya ji a gareni dan ban san komai ba”. A fusace Barrister yay tsalle gabanta yana huci. “Baki san komai ba amma akaje da ke har gida aka kamasu. Karki sha mamakin bayan sanin inda kike har wasu abubuwa na sani a kanki Mss Farishta. Rashin bani haɗin kai kuma na nufin na tonasu kowa yasan ke ɗin wacece har ma da dalilin auren Dawood, sani kankine wannan babban koma baya ne a gareki kuma harma da zuri'arki”. Yayu ta haɗiya masu kauri tana kallon Barrister, sai kuma ta sake wawwaigawa tabbacin dai akwai abinda take shakka. “Naji Barrister zan baka dukkan bayanan da kake buƙata, amma ina roƙonka kabar wajen nan, idan ma zai yuwu kauyen nan gaba ɗaya nake son ka bari. Wlhy na maka alkawarin zan zo na sameka na kuma faɗa maka komai da kake buƙata harma wanda baka sani ba”. “Miyasa bazan sani ba a yanzu?”. “Saboda zamanka anan yana da matuƙar haɗari”. “Taya zan tabbatar da zaki zo ɗin?”. “Na baka dama kabi duk hanyar da zata bibiyi al'amarina”. Kafaɗarsa ya ɗan ɗage sama da faɗin, “Okay inaga bana bukatar hakan, kije kawai ni na san ta hanyar daya dace na bibiyekin. Amma yaushe ne zamu haɗun?”. “Inasha ALLAH a daren yau ka sameni a ƙauyen Jumna”. “Garin su Abu Hanash da Dawood kenan?”. “Insha ALLAH”. Tafiya yake zuciyarsa na faman masa kaikawo akan haɗuwar tasa da Farishta (matar Abu Moosa datazo har gida da ƴan sanda aka kama su Babiy. ALLAH yasa kun gane🥱). Duk da yasan zata iya ƙin aikata abinda ta faɗa na haɗuwar tasu a garin Jimna ya zaɓi barinta su haɗun can bisa lumana. A cikin Hubab ya tsaya yaci abinci tare da sallar azhar. Ya fito masallaci idanunsa suka sake sauka akan wata mota da tun fitowarsa ƙauyen su Farishta ya lura da ita tana biye da shi, sai dai duk da ya ganta suna tafiya kafaɗa da kafaɗa bai kawo komai a zuciyarsa ba. Janyewa yay cike da rashin bama abin muhimmanci ya shige motarsa da zummar zai cigaba da tafiya kawai yaga an zagaye motarsa da bindigu....... ★★★.... ★★.... ★... A firgice ta farka a ɗan barcin daya figeta bayan ta idar da sallar azhar. Ta dafe kanta dake sara mata. Irin mafarkin da tai da dare ne dai babu banbanci. Huci ta furzar da faɗin, “Wace madara ce haka? Tabbas kodaga ina zata fito babu alkairi a cikinta tunda har mafarkin nan ya sake maimaita min kansa. Ya ALLAH”. Ta furta a fili zuciyarta duk babu daɗi, dan zuwa yanzu Iffah ta fahimci wani ɓoyayyen al'amari game da ita, tabbas in har zatai mafarki taita kuma maimaita irinsa sai wani abu ya biyo bayansa mai taɓa zuciya, ta gane hakanne a ɗan zamanta cikin masarautar nan, sai kuma auna abubuwan da suka faru a baya kafin yau ɗin. Sai dai tana ƙoƙarin ƙin gasktama kanta hakan dan kar zuciyarta ta shagala kan abinda zai sakata kaucema umarnin mahaliccinta kuma. Ga kanta jingim kamar yanda yakeyi a duk lokacin datai mafarki makamancin haka, sai zufa data jiƙeta sharkaf tamkar wadda tai wanka. Shigowar saƙo a wayarta da ke gefenta ya sakata tsurama wayar ido na kusan mintuna biyu, kamar wadda aka zaburar wani abu data shafa'a kuma sai ta jawo wayar. Data ta kunna a take tai downloading WhatsApp app..., Bayan ta kammala dai-daita komai tai searching number Sir Fawzan da zuciyarta ke ayyana mata ta fara nema, cikin rashin sa'a taga kusan kwana uku ma baya online ta hanyar lastsin ɗinsa. Duk da hakan bai mata daɗi ba batai wani yunƙurin kiransa ba ta maida akalarta kan number abokinsa Ajmaal. Cikin sa'a shikam dai yana online. Sallama tai masa a taƙaice ta tura, sai dai har kusan mintuna biyu babu reply (yana aiki) zuciyarta ta ayyana mata. Aminta da hakan ya sata cigaba da ajiye masa saƙo kawai a kan duk abinda ya sake faruwa bayan wanda ta tura masa ranar. Daga karshe ta aika masa da roƙon ya bincika mata iyayenta dan har yanzu hankalinta ya kasa kwanciya dangane da su. Ta haɗa masa da adireshin gidansu, da faɗin (In har kaci amanata ko yaudarata na barka da mahaliccin rana da wata yay maka hukunci da alhakin dukkan al'amuran ƙasar ruman da zalincin mulkin wannan shaiɗanin dodo ke tafin hanunsa). Daga haka ta fito shima Sir Fawzan ɗin ta tura masa gajeran saƙo ta goge WhatsApp ɗin gaba ɗayansa ta ajiye wayar. Da ɗan layin nauyin jikin dake tare da ita ta miƙe, tana ƙoƙarin shiga toilet taji kamar an gitta mata ta baya. Idanunta ta ɗan rumtse sai kuma ta waigo. Komai babu dai a zahiri dan haka ta kaɗa kanta kawai ta shige bakinta da addu'a.... Fitowarta kenan bayan ta watsa ruwa alerm ɗin ƙofar yay ƙara alamar ana knocking. Sai da ta zira doguwar rigar abaya data ɗakko cikin kayanta sannan ta ƙarasa ƙofar ta buɗe. Hadimar dake tsaye ta zube ƙasa cikin girmamawa tana kwasar gaisuwa. Amsa mata Iffah tai, zuciyarta babu daɗi akan yanda suke ƙasƙantar da kansu, ta amsa cikin sauƙin muryarta dake a sanyaye sakamakon mafarkin da duk ya sakar mata kasala.. “Wani abu ya faru ne?”. Ta tare hadimar tunkan tace komai. Kai ta gyaɗa mata tana sake rissinar da kanta. “A gafarceni ya Zawjata-almilk. Dama abinci ne aka kawo daga sashen mai Babban ɗaki”. Iffah tai ɗan jim tana hasashen wace kuma mai babban ɗaki? Kamar hadimar ta fahimta tai saurin mata fashin baƙi da “Malikat mai babban ɗaki”. (Malikat Haseenat) shine abinda zuciyarta ta ayyana mata. Ta kaɗa kanta da faɗin, “Okay ba damuwa zan fito”. Daga haka ta maida ƙofar ta rufe. Ciki ta koma, sai dai maimakon zama sai ta koma kaikawo kamar mai Safa da marwa abubuwa masu yawa na faman mata kaikawo. Ta jima a haka sosai kafin ta sake kimtsa jikinta cikin wata tsadadiyar abaya mai adon stones dake ta ƙyalli da ɗaukar idanu. (Wannan yana cikin horon Daneen Ammarah data tabbatar mata koda wasa karta zauna da kazamar shiga ko fitowa da ga ɗaki a raguwar kwalliya. Dolene inhar zata bar cikin ɗakinta ta tabbatar komai na jikinta ya isa a kalleta da shi. A tsarin masarautar hakan ba fariyya bane mutunta kaine ga kowa. A kuma ɗan zaman Iffah cikinsu ta fahimci hakan sarai). A yanzu ma kamar ɗazun turarrukan sa ta baza har ƙamshinsu na rige-rigen fita kafin ita ta fita. Ta fito cikin takunta na nutsuwa da ƙasaita kamar wata budurwar macen ɗawisu (🥱😉lol)..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_35_* ........Hadiman sashin gaba ɗaya kamshin turaren da sukaji ya sakasu tunanin Tajwar Eshaan da bai jima da shigowa ba daga fada ne ya sake fitowa. Sai kuma sukaga saɓanin haka lokacin da Iffah ke ƙarasowa cikin katafaren falon mai ɗauke da duk wani nau'in kayan more rayuwa irin na wanda suka isa. A kujerar da ko ba'a faɗaba tsarin zubinta ya isa tabbatar ma mai kallo Shahan-shan ne kawai ke zamanta ta kai zaune da bismillah a bakinta. Ƙafa ɗaya kan ɗaya ta harɗe fiye da salon sarauniyar Ingila tana kallonsu. Cikin rawar harshe dajin kwarjininta ya cike falon tsaf suka shiga zubewa suna gaisheta. Yatsu biyu ta ɗaga musu cike da ƙasaita batare data amsa ba dan haka kawai yanayin da ta tashi da shi taji bata buƙatar magana. Basu iya sun motsa ba har ta gama zuƙar iska da fesarwa tamkar mai lissafin kaɗawarta sannan ta dubesu, sai kuma ta maida ga tarin abincin da aka shirya yanzu akan wata lallausar darduma saɓanin na ɗazun akan teburin cin abinci. Akan farin tambulan na gilashi mai ɗauke da madara fara ƙal-ƙal ta sauke idanun nata (mafarkina ya zama gaskiya kenan ko saɓaninsa) zuciyarta ta ayyana har lokacin idanunta tsaye akan tambulan ɗin.. Hadiman da basu fahimci ma'anar kallon da takema kayan abincinba cike da girmamawa a gareta ɗaya ke faɗin, “Ya Zawjata-almilk abincine daga saken mai babban ɗaki, an shiryashi ne matsayin liyafa gareki ke da shugaba”. A hankali Iffah ta janye idanunta daga wajen ta maida kan hadimar na tsahon wasu sakkani, acan ƙasan zuciyarta kuwa nanata sunan Malikat Haseenat take tamkar mai bitar karatun hadda. Batare da tace komai ba kuma sai ta kaɗa kanta. Shiru ya sake biyo baya kafin Iffah ta katseshi da duban hadiman da har yanzu dai ke tsaye da alama zaman jiransu sukeyi kenan, dan ta fahimci idan zaici abinci haka suke zagayesa. Kanta ta kauda da faɗin, “Maleek fa?”. Kai tsaye duk suka fahimci wa take nufi, tunda dai duk sun san minene ma'anar kalmar Malik ɗin. Cikin tsantsan da kai ɗaya daga ciki ta amsa mata da “Yanzu ya shigo daga fada”. Bata amsa ba, sai ɗan jimm da tai na tunani akan ambatar fada da hadimar tayi, amma a zahiri ta basar abinta. ★Kasancewar saƙon haɗa liyafar cin abincin na Malikat Haseenat da tai akan iya shi da wadda ake kira matar tasa ya riskesa tunma kafin Iffah, dan kusan shine ma yay sanadin barowarsa fada duk da Aaminsa Miran Jasim (Aami. Kawunsa)ya buƙaci zaman tattaunawa da shi. Badan son ransa ba ya kimtsa ya fito cikin shiga mai sauƙi ta zaman gida. Kamshinsa da takun sawayensa dake tabbatar da girman ikonsa tuni ya iso a kunne da hancin Iffah dama hadiman dake zagaye da ita. Tuni hadiman duk sun zube bisa gwiwunsu kawuna a ƙasa dan kallon shugaban nasu kai tsaye haramunne garesu bisa al'adar masarautar, idanma hakan ta faru gaban Ghazi zaka iya fuskantar tsatstsauran hukunci a dalilin hakan. Akanta dake harɗe kan kujerar da bayan shi babu wani mahaluki daya iya kwatanta zama kanta ya fara sauke ƙasaittun idanunsa. Dai-dai itama ta ɗago nata sakamakon jin takun sawayensa da zubewar hadiman. Cikin ido suka kalla juna, hakan yay matuƙar tsikarar zuciyar Iffah da abinda take faman hasashe da neman tabbaci a kwanakin nan ya tabbata ɗin yau a idanunta. Dan tabbas shigar jikinsa ta yanzu ta sake tabbatar mata da waccan fuskar... Shine ya fara janye nasa kausasan idanun batare data iya tsinto komai a cikinsu ba. Kamewa da gagara fassara abinda ke kan fuskarsa kuma ya taka rawar gani wajen ɓoye ainahinsa. Sai ma kallonsa da ya maida kan ƙaton agogon dake kafe a falon cike da basarwa kai kace bai ganta bane. Ita madai basar da shi ɗin tayi kamar ma bata san da fitowar tasa ba, sai zuciyarta dake faman kai kawo a ƙirjinta cikin sauri-sauri. So take ta gaskata shi ɗinne kota ƙaryata amma zuciyarta taƙi bata haɗin kan karkata akan ko ɗaya a cikinsu. Sai ma neman jefata a ruɗani takeyi...... *_BARRISTER_* Duk yanda Barrister yaso sanin suwaye su? Mi kuma yay musu basu saurareshi ba suka turasa cikin jibgegiyar baƙar motarsu, yayinda ɗaya daga cikinsu kuma ya shiga motar Barrister ɗin ya fiddo komai na ciki a cikin wata ƙatuwar jakka suka bar wajen.. Suna ɗan matsawa a wajen wani abu mai masifar ƙara ya ziyarci kunnuwan kowa. A take aka fara gudun ceton rai dan duk wanda yasan bomb yasan shine a yanzun ma. “Innalillahi wa inna'illaihirraji'un”. Barrister ya faɗa idonsa nabin motarsa da tai sama ta shiga dawowa pieces ƙasa alamar dai bomb ɗin daga cikinta ya tashi. Duk da ya firgita da mutanen yay jarumtar dubansu fuska a dake. “Ku su waye? Miyasa kuka aikata min haka?”. Babu wanda ya tanka masa a cikinsu, kamarma basu jisa ba sukayi. Hakan sai ya ƙara tada hankalin Barrister, dan ya fahimci ya shiga hannun mugayen mutanen nan kenan. Yunƙurowa yayi da nufin ƙara magana suka jefa masa handkherciff a fuska, daga haka bai sake sanin inda yake ba sai buɗe idanu yay ya gansa a wani ɗaki da bai san inane ba... Gaba ɗaya jihar Hubab da ƙasar Ruman a rikice ake akan tashin wannan bomb, dan abune da bai taɓa faruwa da su ba. Jami'an tsaro sun iso akan lokaci, sai dai Alhamdullah ba'a samu asarar rai ko ɗaya ba daga mutanen gari, amma ana tunanin harda drivern motar al'amarin ya rutsa saboda babu wanda ya lura da sanda mutanen nan suka ƙwamushe Barrister ɗin kasancewar komai sun yisa ne cikin ƙwarewa... Jami'an tsaro da ƴan jarida tuni sun iso wajen akan lokaci, hakama jama'ar gari masu jarumta sun zagaye wajen domin ganema idanunsu. Babu gawar direban motar a duk iya bincike da jami'an tsaro sukayi, dan basu ga wani alamar sassan jikin mutum ba ko ɗan yatsa, hakan sai ya ɗaure musu kai dan mutanen da abun ya faru a idonsu sun tabbatar sunga lokacin da mai motar ya ajiye ta a wajen ya shiga masallaci, koda aka fito kuma mutane da yawa sun tabbatar sunga lokacin daya nufi motar wasu ma sunce har ya shiga. Wannan zance ya sake ɗaukar hankalin jama'a kowa yana faɗar albarkacin bakinsa akan al'amarin... Isowar wasu samari wajen kusan dai-dai da tashin bomb ɗin, kallon juna sukai da sakin dariya a tare suna tafawa. Sai da sukai mai isarsu drivern dake jan motar ya ɗauka waya. Nuni yay musu da suyi shiru. Take motar tai tsit kuwa. Ya ɗan rissina cike da girmamawa tamkar yana a gabansa ne yana kwasar gaisuwa, bai damu da a yanda aka amsa masa a daƙile ba ya cigaba da faɗin, “An rufe babinsa ranka ya daɗe”. Murmushi yayi alamar an amsasa da magana mai daɗi daga can. Sai kuma ya sauke wayar da juyawa yana kallon ƴan uwansa ya kashe musu ido. Dariya suka shiga kwasa a yanzun ma, bayan sanyi wadda suka gamsu sun wadata sannan suka fita suma suma shige cikin taron mutanen dake wajen dan jin mi'ake tattaunawa..... ★★★..... MASARAUTA ★..... Sai da ya kai zaune a inda aka shirya tarin abincin da kusan minti biyu sannan ta motsa itama dalilin maganar da Hadimai sukai mata. Bata musa ba ta miƙe zuwa inda yaken cikin takunta na nutsuwa da wasu ke ɗauka yanga ko makamancin hakan. Zama tai irin nasa na ƙasaita sai dai da alama ita kanta bata fahimci tayi hakan ba ma. Tsaurin idonta ya sakashi dubanta ta gefen ido batare da alamar hakan ta bayyana a yanayinsa ba. Tuni hadiman suka ƙaraso domin shirya abincin garesu. Iffah batai yunƙurin hanasu ba, dan a ganinta dole ta nutsu ta fara fahimtar yanda ake masa komai kafin ta karɓa wannan tsarin shima. Ta ɗan bi madarar da hadimar ta ɗauka, har yanzu zuciyarta na mata wasiwasi akan madarar batare data san dalili ba... “Bar nan”. Ta faɗa dai-dai Hadimar na yunƙurin zuba madarar a ƙaramin cup na glass daya gama haɗuwa. Cikin mamaki hadimar ta sake risinar da kai domin girmamawa ga Iffah tana faɗin, “Ya Zawjata-almilk madara na ɗaya daga cikin abinda shugaba yafi buƙatar amfani da shi a irin wannan lokacin”. Kai tsaye babu ko ɗar tattare da Iffah tace, “Na yau dai bazai sha ba. A ɗaukesa anan”. Tsoro ne ya bayyana sosai a fuskar hadimar, gashi bata da damar ko satar kallon sashin da Tajwar ɗin yake balle ta fahimci karatun tasa fuskar. A ɗan ɗar-ɗar na rashin madafa ta ajiye tambulan ɗin a gefe ta ƙarasa aikinta. Duk da abinda ake yi a gaban Tajwar Eshaan ne, yanaji kuma yana gani. amma tsabar miskilanci da ƙarfin iko irin na masu ƙasa a hannu bai ko motsa ba balle bada wata alama akan abinda Iffah tayi ya bashi mamaki, ko ya ɗimautashi, koya birgesa, koya bashi haushi. Ko ɗaya babu mai iya tsinta a yanayinsa. Iffah ma dai bata yarda ta dubesa ba balle ta tsinta komai a tattare da shi ɗin. Sai ma wani kallon da taima hadiman ya tabbatar musu bata bukatarsu a wajen. Dan haka tuni suka ɓace tamkar ƙyaftawar ido. Ya ɗan ja wasu mintuna zaune batare da ya taɓa komai ba, Iffah ta ɗan laɓe baki, acan ƙasan maƙoshi ta furta “Ranka ya daɗe barka da wannan lokaci”. A hankali ya ɗago ya zuba mata idanunsa, a mamakinsa bashi take kalloba ma. Kuma ya tabbatar itace tai maganar ba wani ba dai. Sake tsukewar fuskarsa mai cike da gizago da motsa hanunsa dake kan spoon ya tilasta Iffah ɗan ɗagowa garesa. Sai kuma ta tsaya cak tare da ɗago birkitattun idanunta da ƙyau. Cikin nasa dake kallonta suka shige tamkar ya tsara hakan da gayya. Muƙut ta haɗiye yawu da ƙoƙarin kame rauninta dake neman bayyana a fili ta kauda kai gefe.. Shima nasan ya janye a ƙasaitance ya fara cakulal abincin kamar mai cin magani batare da ya amsa mata gaisuwar tata ba. Hakan da yay ya sosa zuciyar Iffah, dan haka ta kumbura fuska lips ɗinta suka shiga motsawa alamar akwai magana a bakinta sai dai babu damar faɗa... ★★.... ★.... Tun bayan tabbatar da madarar ta shiga jerin abincin liyafar da aka shiryawa Shahan-shan da Zawjata-almilk ta kasa zaune ta kasa tsaye, bukatarta kawai taji sakamakon da take buƙata ga amintacciyar hadimarta akan lokaci. Sai dai kuma shiru kakeji wai malam yaci shirwa har lokacin da labarin tashin nakiya a jihar Hubab ya iso cikin masarautar. Ba wannan ne a gabanta ba, dan haka cikin jan tsaki ta kashe television ɗin a harzuƙe. Idanunta ta sake maidawa kan agogon falon tanaji kamar tai tsalle ta ganta a sashen Tajwar Eshaan ɗin ayita ta ƙare. Dan yanzu a duniyar nan gani take bata da babban maƙiyya sama da yarinyar nan datai mugun shige mata hanci amma ta gagara fyatota ta huta a dalilin gargaɗin Uwa data kasa gane manufarsa har yanzu. Sai dai yarda da Uwa ɗin ya tilasta mata bin komai ɗin a sannu. Zata iya rantsuwa tunda ta san kanta bata taɓa cin karo da abinda ya kiɗima zuciyarta ba irin saƙon Zawjata-almilk na raye bayan ta kwana a turakar Shahan-shan kuma. Ba ita kawai ba, hatta Uwa hakan ya kiɗimata da sake tabbatar da yaƙine na gaske tsakaninsu da wannan yarinyar kenan. Dan haka batai wani magana mai tsaho da Ta-kurya ba bayan bata umarnin a isar da madarar data bata ga Iffah ta ɓace cikin tsanani ɓacin rai daya ƙara birkita dukkan tunanin Ta-kurya ɗin a yanzu har ta kasa zaune ta kasa tsaye sakamakon hakan........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_36_* ........Isowar labarin tashin nakiya a jihar Hubab ya matuƙar tada hankalin duk wani mai faɗa a ji a daular ruman. Dan abune da bai taɓa faruwa ba a kasar ta ruman. Amma abin mamaki ga Tajwar Eshaan ba hakan bane, dan babu wani alamar damuwa ko nuna kaɗuwa da lamarin. Kallo ɗaya yayma akwatin talabijin ma ya ɗauke kai kamar ba'a ƙasar da yake mulka matsayin shugan kowa da kowa al'amarin ya faru ba. A karan farko wani abu da tun shigowar Iffah masarauta bataji akansa ba ya tsikari zuciyarta sakamakon ganin halin da ya nuna akan wannan al'amari da duk wanda ya kwana ya tashi a ƙasar ta ruman bazai ce bai shiga ruɗani ba. Duk da ance ba'ai asarar rai ko ɗaya ba taji kamar ta tashi ta shaƙure wuyan Shahan-shan ɗin ta huta da ganin wannan azzalumin shugaba da kansa kawai ya sani sai ahalinsa. “Mi hakan ke nufi?”. Ta faɗa tana faman kai kawo a ruɗe itama duk da a labarin an sanar da ba'a samu asarar rai ko ɗaya ba sai dai dukiya. Abu mafi caja ƙwaƙwalwa ga kowa ma ba ita kaɗai ba shine jin wai wanda ya dasa bomb ɗin ya tsere Bayan wasu sun tabbatar da sunga fuskarsa da shigarsa motar, musamman ma wasu samari huɗu da suka tanbatar da tare suke da wannan mota tun daga ƙauyen Lufana da alama mutumin daga can ya fito. Tabbas sai tayi ajalin wannan mutumin a zuciyarta zataji salama. Dan a ganinta idan yau ya tashi kowa bai rasa ransa ba na gobe kuma fa? A wannan gaɓar ta fara zargin anya wannan sarkin bada wata manufa dama ya dawo ya karɓa mulkin mahaifinsa ba? Dan alamu sun fara nuna uban nasa ma shine ya kasheshi. “Lokaci yayi da zan fara aikina gadan-gadan”. Ta faɗa a zahiri cikin tabbatarma kanta da yanayin ɗaukar alwashi.... (Muma kam muna bayanki Iffah, dan muna son sanin mike zuciyar wannan bahagon sarki haka mai wahalar fahimta😉🥱🏇). ★★★ A babban zauren majalisan manyan masu faɗa aji na daular ruman kuwa na can yana neman hargitsewa dangane da faruwar wannan al'amari. Kowa faɗar albarkacin bakinsa yake a duk yanda zuciyarsa ta ayyana masa musamman masu sukar mulkin Tajwar Eshaan a fakaice. Duk wannan kace nace da akeyi Tajwar Eshaan ɗin na zaune cikinsu amma uffan bai tofa ba har suka ci suka tsire. Sai da suka lafa dan kansu da kuma maganar Miran Arshaan cikin ɓacin rai a garesu sannan Tajwar Eshaan ɗin ya buɗe idanunsa dake a lumshe ya gama ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya.. Akan Miran Arshaan dake cigaba da faɗa rai ɓace kan kausasan maganganu nasu ga ɗan ɗan uwansa kuma sarkinsu a yau basu dace ba ya sauke idanunsa. Cikin muryarsa mai zurfi da ƙasaita ya fara magana a gadarance kuma a fisge... “Barsu Aami. Waninsu bazai canja komai ba, kamar yanda bazai tirsasa Eshaan yin komai ba. Abinda kawai nake son ku sani, Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed guguwace data gama turniƙeku, kuma babu ruwan kogin da zai iya shayar da ita ruwan da zata lafa. Ku daina bama kanku wahala ƙasar ruman da jama'ar cikinta a rubuce suke tsakkiyar tafin hannuna. Idan na murza kwafsanku kawai duniya zata gani a cikin guguwata, idan na matsa, jininku ne zai dinga ɗiga a ƙarƙashin sawun ƙafata na ringa bi ina takawa matsayin kwalta, ya rage naku ku zauna a inda na baku zaɓi ko ku zaɓo mummunan ƙaddararku da kanku tun lokacin ɓacewarku a doron ƙasa baiyi ba”. Yana gama faɗa ya miƙe cike da takun Izza da kasaita ya bar falon. Da kallo duk suka bishi ran wasunsu na ƙuna, zukatansu kam tamkar zasu kifo ƙasa dan firgici. Cikin dauriya da nuna jarumta wani ƙyamusashen dattijo da tsufansa ya fara bayyana a cikinsu yay ƙwafa rai ɓace da kausasa murya. “Lallai wannan yaron ya cika ya tumbatsa kuwa. Wai kenan haka zamu cigaba da zama yaro ƙarami na tafka kuskure da mulkin zalunci yana kuma takamu a yanda ya gadama. Akaf tarihin mulkin daular ruman ba'a taɓa tsageran yaro kamar wannan ba, amma ubansa ya ɗaura shi matsayin Shahan-shan bayan babu mai makamancin shekarunsa daya taɓa zama a wannan matsayin. lokaci yayi da zamuyi bore wajen tsigesa kafin ya gama halaka ƙasar baki ɗaya tunda naga shi ran ɗan adam ba'a bakin komai yake garesa ba. wama ya sani ko shine yasa a dasa nakiyar kamar yanda ya kashe ubansa da ƴaƴan mutane da aka aura masa. Koda yake minene ma na tantama tunda ga amsa ya bamu da bakinsa cewar ƙasar da ƴan ƙasar duk a tafin hannunsa muke”. A zahiri dai kowa yay tsitt yana sauraren dattijon, amma a zukatan wasunsu farin cikine fal da zantukan wannan tsoho ga Tajwar Eshaan ɗin da mafi yawansu shakkarsa ta gama zagaye tunaninsu duk da kuwa kusan duk sun haifesa dan babu wani sa'ansa, dan har yanzu tun ƴan majalissar mulkin mahaifinsa ne bai canja ba. Dattijon na rufe baki Miran Jasim ya miƙe rai a ɓace shima. Dattijon ya watsama wani mummunan kallo da faɗin, “A lallai ka cika dattijon banza dan bazan kalleka matsayin Aami ɗinmu ba yau kam. Mun godema ALLAH daya fara nuna mana ku a zahiri, ai bamu san ɗan ɗan uwanmu ya kai muku har haka a zuciya ba sai yanzu. To ku sani duk ma mai irin wannan tunanin ya makaro, Eshaan kuma a gareku sai gani sai hange sai hararar nesa, dan badai mutum ba ku rubuta ku aje”. Ya kare maganar yana ɗan ƙyaftama Miran Arshaan daya saki baki tsabar al'ajabin ɗan uwan nasa da kasa fahimtar inda ya dosa. Cikin sauri ya kaɗan kansa da amshe zancen a fusace shima yana miƙewa. “Aam ai ban san haka kakeba wlhy sai a yau, ashe zaka zama na farko a jerin wanda zasu soki jinin Haysam Akhi kuma ɗan uwanka mahaifinmu dan ƙasa ta rufe idanunsu? To bazamu ce da ku komaiba a yanzu, amma kusani duk wanda yake da wannan ƙudirin a ransa jininmu fansa ne ga kare Eshaan tako wace fuska. Mun barku lafiya”. Waɗan nan zantuka na Miran Jasim da Miran Arshaan sun matuƙar saka ruɗani a zukatan duk wanda ke a wannan zauren taron. A take wasu suka shiga barranta kansu ga wannan magana ta dattijon Aamin sun ganin waɗanda ma ya dace suyi hanƙoro da kwarema Tajwar Eshaan ɗin baya saboda kwaɗayin kujerar da yake kai tunda suma sunada hakki a kanta na tare da shi su kuma a wa. Anan fa rikici ya kaure aka tashi baram-baram.... ★★ “Nikam na kasa fahimtar dalilin ka nayin hakan”. Miran Arshaan ya faɗa bayan fitowarsu daga zauren tattaunawar. Wani shegen murmushi Miran Jasim ya saki cike da basarwa. Sai da sukai nisa da sashen Tajwar Eshaan gaba ɗaya sannan yay wata ƴar dariya batare daya kalla Miran Arshaan ɗin ba. Shimfiɗa kenan daga cikin plan b, harinmu na gaba shine ƙulla alaƙa da yarinyar nan, dan na san yanzu abinda zatai yinƙurin farawa shine bincike akan wanene shi”. “Wai ya akai duk kake sanin hakan?”. Miran Arshaan ya tambaya cikin mamaki. Dariya Miran Jasim yayi sosai da faɗin, “Arshaan Akhi har yanzu kai ɗin yaro ne. Waya gaya maka mai nema yana zaman jiran tsammani. Tashi yake da ƙwanji da zuciya wajen samowa ai. Karka damu da inda na sani, kai dai kawai ka tabbatar littatafan nan da mukai magana kwanaki an kaisu books room an ajiye a daren yau, dan bana raba ɗayan biyu zuwa gobe zata iya bukatarsu”. Cikin halin ko'in kula Miran Arshaan ya ɗage kafaɗu da tabe baki, sai dai acan ƙasan ransa dariya yake dan shima akwai nasa shirin akan hakan tun randa sukai maganar...... ★★ Duk da fuskarsa mai tsananin ɓoye sirrin zuciyace a yau ɓacin ransa sai da ya bayyana. Huci kawai yake faman furzarwa a kai-akai. Dan daga ɗakin meeting ɗin nasu da ba'a samu damar tattauna abinda ya dace ba kai tsaye sama yay can ƙarshen rufin ginin sashen nasa da aka gyara domin hutawa kawai. Ko gaisuwar hadiman dake tsare da ƙofar shiga wajen baiyi ba. Ya jima yana faman kai kawo hannayensa zube cikin aljihun farin wandonsa. Bakajin komai tattare da shi sai shaƙa da furzar da numfashi. Sai da ya ɗan samu nutsuwar da yake bukata ya zaro waya dake cikin aljihunsa. Kira yay, bugu ɗaya kuwa aka ɗaga, batare daya amsa gaisuwar da ake masa ba a kausashe ya furta. “A sakaya min shi, inda babu wani mahaluki da zai taɓa hasashe a kansa”. Yana gama faɗa ya yanke kiran cikin sake tsuke fuska da zuƙa ya fesar..... (Anya kuwa....?? 🤭bakina kanen kafa ta dai🏇). ★★ A ɓangaren Iffah tana tsaka da kai kawonta da ƙullawa da warwarewa itama wani tunani ya sata tsayawa cak. Miƙewa tai cikin gamsuwa, sai kuma ta koma ta zauna bisa wani tunanin da yazo a bayan wanda ya sata mikewar. A kallo ɗaya zaka fahimci tana cikin yanayin da duk wani ɗan ƙasar zaka iya ganin ya shiga sakamakon wannan baƙon al'amari daya shigo musu. Da farko bai lura da ita ba saboda idonsa rufe yake da ɓacin rai har lokacin, sai da ya kai zaune yay ƙoƙarin lumshe ido sai kuma ya buɗesu a kanta dai-dai itama ta kallesan mamakin yanayinsa na yanzun kuma fes a fuskarta. Ita ta fara janye nata shima sai ya furzar da huci mai zafi yana maida nasa ya lumshe kamar yanda yayi a farko. Falon ya ɗauka shiru babu alamar wani zai tanka sai karar na'urorin ac dana tv da har yanzu ake cigaba da nuna al'amarin da yanda hankulan jama'a ke tashe. Kiran sallar la'asar ne ya katse zaman shirun nasu. Iffah ta fara yunƙurawa ta tashi batare da ta ko sake kallonsa ba dan da gaske har cikin rai haushinsa takeji yau. Da kallon ƙasan ido ya bita harta ɓacema ganinsa. Ya ɗan sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya da maida idanunsa ya rufe. Sai da Iffah tai kusan mintuna huɗu da barin wajen sannan ya mike shima har yanzu da alamar ɓacin rai tattare da shi.... ★★★.... Bayan Iffah ta idar da salla kamar yanda ta tsara tai shirinta tsaf cikin wata doguwar riga mai tsananin ɗaukar idon duk wanda zai iya kallonta. Kamshin data gaje batare da umarnin mai shi ba ta baza tamkar tayi ɓarinsa a jikinta. A cikin dukkanin shirinta babu bijirema umarnin waɗan da tazo wannan matakin a dalilinsu, dan haka kai tsaye tai kiran number Daneen Ammarah. Ana ɗagawa tai sallama cikin sauƙaƙa murya mai nuna ladabi. Daga can Daneen Ammarah ta amsa cike da zumuɗi da nuna jin daɗinta da wannan kira. “Shahrbano ce da kanta haka?”. Murmushi Iffah tai mai bayyana haƙora jin sunan da Daneen Ammarah ta kirata da shi. Ta girgiza kai tamkar tana a gabanta. “Mamy zakisa a tsire ni a tsakkiyar daular ruman fa”. Dariya sosai maganar ta bama Daneen Ammarah. Dan haka ta dara sosai kafin ta tsagaita. “Waya isa ya tsire Ibnati kuma Shahrbano duk faɗin ƙasar ruman. Babu mai wannan power ɗin Ibnati, ko maƙiya sun san kin gagara sai kallo daga nesa, dan kowa ya tabbatar a yanzu ke ɗin ce _Lady of the city_”. Komai Iffah bata iya tace ba, sai dai Daneen Ammarah na iya jiyo sautin murmushinta harta gama kwarzantata. “Mamy dama na kiraki ne na shaida miki ina ɗan son na fito zama waje ɗayan ya isheni, daga nan sai na ɗan leƙama ɗakin karatu kozan samo abin ɗebe kewa”. “Hakan kam yana da ƙyau Ibnati. Dan haka ki shirya kawai, hadimanki na sashenki za'a sanar da su su tsumayi fitowarki”. “Nagode Mamy, ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsohon rai mai amfani da albarka”. Cikin jin daɗi Daneen Ammarah ta amsa da Amin tana mai saka mata albarka itama. A yau kam Iffah ta ƙara tabbatar da tsantsar ƙarfin ikon mulkin wannan daula. Dan tunda ta baro hawa na ƙarshe hadiman sashin na Shahan-shan ke faman zubewa gabanta batare da dubi da ƙanƙantar shekarunta ba, matsayinta kawai suke kalla. Duk sai taji zuciyarta babu daɗi ganin kusan duk shekarunsu zai iya kaiwa dai-dai dana Hanash, wasu ma sun girme masa. (Nace Iffah danma Tajwar Eshaan yayi sauyi ne da matasa kikaga hakan, da har sa'an kaka da Babiy sai kin gani kuwa). Kamar yanda Daneen Ammarah ta faɗa tako samu hadiman na zaman jiranta. Ta gane hakanne ta hanyar zuwa da sukai suka zube a gabanta da sanar mata matsayinsu. Batare da damuwa ba duk ta bisu da kallo, su biyar ne cif kuma duk yara ƴammata matasa, za'a iya samun sa'aninta dama wanda suka girme mata kamar su Fariha. “Ina buƙatar zuwa books room ne akwai wani tsari akan hakan?”. Da sauri ƴar babbar dake ta gabanta sosai ta girgiza kai. “Ga Zawjata-almilk babu wani dokar yin hakan ALLAH ya ƙara miki lafiya”. “Okay zamu iya tafiya”. Iffah ta amsa mata kai tsaye. Hadima ɗaya ce tai gaba sosai Iffah na biye da ita cikin takunta na nutsuwa da wasu kan iya gani su fassara da abinda zuciyarsu ta basu. Bayanta Hadimai huɗu na biye da ita cikin taka tsantsan da nuna girma da ƙarfin ikonta a bayyane...........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_37_* .........Duk ta inda suka gitta kwarjininta dake ɓoye shekarunta kansa a bata girma irin wanda ya dace ga Zawjata-almilk da suka isa a masarautar. Hadimai kam sai zubewa suke bisa gwiwunsu sakamakon sanarwar da ɗan kazagin da Iffah bata farga da shi ba sai da suka fara tafiya taji shelanta tahowarta da yake yi. A yau kam ta ƙara jinjinama girman wannan katafariyar masarauta mai abubuwan kallo matuƙa. Sai dai ga mai kallo bazai taɓa fahimtar hakanba a yanda take faman basarwa kai kace ita ɗin tun fil'azal jinin sarauta ce. Ba wani nisa bane zuwa books room ɗin, hakan ya sakasu isowa cikin ƙanƙanin lokaci dan ma tafiya ce ta ƙasaita.... Cikin ƙankanin lokaci labarin fitowar Zawjata-almilk ya karaɗe masarautar. Hadimai ƴan leƙen asiri dake watse ta ko'ina sun gama kai labari ga iyayen gidansu. Da yawa mamaki ya kamasu tare da gane lallai yarinyar tazo da tsageranci. Inba tsageranci ba wace Zawjata-almilk ce ta taɓa fitowa bayan kaita turakar Shahan-shan da kwana ɗaya kacal. Wasu kuma kai tsaye fassara wannan fita suke da gatsali, acewarsu Iffah nason tabbatar musu tafi ƙarfin iyawarsu, ƙarfin ikon su kuma ba komai bane dan ta gagaresu. ★Malikat Bushirat kanta isowar wannan labari a kunenta sai da tai wani tsamm na nuna mamaki, sai dai bata ce uffan ba kasancewarta mace mai tsananin jin kai da izza. Tana son Iffah, kuma ƙarfin halin yarinyar na kawatar da ita. Sai dai hakan ba yana nufin zata dama damawarta ne a yanda taso ba ko ƙetare tsarin zama a masarautar musamman ga Zawjata-almilk irinta da ƙa'ida komai sai da umarnin Malikat zatayi sa. (Kamar dai ita dake mahaifiya ga Tajwar Eshaan. A ƙa'ida dole komi Iffah zatayi sai ta nema izinin mahaifiyarsa kafin ta aiwatar). Jin al'amarin ya cigaba da caccakar zuciyarta ta sallami duk hadimanta. Kamar ƙiftawar ido suka ɓace kuwa. Rai a ɓace ta ɗaga waya tai kiran Jasrah da ita bama tasan wainar da ake toyawa a masarautar ba kasancewar a ɗan tsakanin nan tana fama da laulayin ciki ne sama-sama. Duk da a halin rashin jin daɗi da take ciki bazata iya ƙin amsa kiran ƴar uwar tata da takema kallon uwa a yanzu ba. Haka ta kimtsa cikin dauriya ta nufi sashen Malikat Bushirat ɗin. A tsaye ta sameta cikin yanayin ɓacin rai da ya kasa ɓoyuwa a kan fuskarta. Sai duk taji itama nata ran a jagule... “Akia kina lafiya kuwa? Miya ɓata miki rai haka har fuskarki ta kasa ɓoye wa?”. Malikat Bushirat ta zuƙa kakkaurar iska ta fesar tana mai kallon ƴar uwar tata. Cikin ɗacin murya tace, “Yarinyar nan ce”. “Yarinya kuma? Wace yarinya kenan?”. Kamar bazata tanka ba, tai taku ɗaya zuwa uku batare data dubi Jasrah ba tace, “Zawjata-almilk. Da alama tana buƙatar sai an saita mata zama da tuna mata nan daular ruman ce ba getto eria ɗin data rayu ba. Komai muna yinsa da ƙa'ida bisa umarnin na gaba”. “Kiyi haƙuri Akia. Amma na kasa fahimtar miya kawo wannan maganar, wace kuma Zawjata-almilk ce a cikin yaran? Dan nasan dai kinfi kowa so da ƙaunar wadda ke tare da shi a halin yanzu”. “Ina sonta bashi zai bata lasisin shimfiɗa abinda ta gadama na a saman nawa ƙarfin ikon ba. Yanzu labari ya iso gareni ta fito daga sashen Saiful-malik zuwa books room tare da hadimai”. “Tofa, ita kuma da wannan tazo? Mu muna murnar samunta matsayin wadda zata share kukanmu amma zata fara da haka?. To amma fa Akia wani hanzari ba gudu ba. Shin baki ganin salon yarinyar a wani mahangar nasara ce a garemu. Na farko dai babu wanda yasan ta fito ne batare da umarninki ba. Na biyu koba komai ta sake jaddada isar da saƙonmu akan maƙiya. Na uku salonta tamkar barazana ce ga duk wani shu'umi dake rayuwa a wannan masarautar. Inaga bai kamata ki damu ba, dan a wani ɓangaren ma kamar mune masu laifi, karki manta Mammah ta mikata sashen Abni batare da bin ƙa'idojin da ake kai Zawjata-almilk turakarsa ba. Sannan inada tabbacin ba'a sanar da ita komai game da tsarin komai ba fa, sai aikin da muka faɗa mata zatayi a garemu”. A hankali Malikat Bushirat ta saki wata nannauyar ajiyar zuciya. Cikin kwantar da murya ta ce, “Hakane kumafa Jasrah, kin tunatar da ni abinda ya ɓacemin har idona ya rufe. Sai yanzu na fahimci lallai wannan fitar tata ma da alama tanada manufa akan umarnin aikinmu. Duk Mamma ce da wannan kwamacalar da muka kasa fahimtar manufarta a kai, nayi niyyar zuwa sashen nata ma naji dalili baƙin nan na ɗazun suka cinyemin lokaci. Amma munyi magana da Ammarah zuwa anjima zanje ko cikin ɓadda kama ne”. “Hakan yayi, dan koni ina son sanin yaya akai hakan ta kasance. Duk da dai Alhamdullah yarinyar ta kuɓuta. Amma mun kwana a fargaba ai dan ko barci jiya banajin waninmu yayi wlhy. Hatta da Abu Harith kwana yay tunani”. Murmushi Malikat Bushirat tayi, dan har cikin ranta tana ƙaunar ƙanin mijin nata kuma mijin ƙanwarta, tare da yaba ƙoƙarin sa akan kulawa da kaunar da yake nunawa ga gudan jinin nata tilo da har wasu ke jin zafinsa a gidan bisa hakan..... ★★.... Katafaren ɗakin daya kasance mai cika ido ga Iffah tsarinsa ya matuƙar ƙawatar da ita. Ta samu jagorancin shiga lungu da saƙo na cikinsa bisa taimakon masu kula da ɗakin. Inda a zagayen nasu suke nuna mata abubuwan tarihi na tun farkon ƙarnin kafa Daular ruman ɗin da suka shuɗe cike da girmamawa a gareta. Tafiya kam mabuɗin ilimice haƙƙun dan Iffah ta ilmantu da abinda yafi wanda ta sani ƙalilan a baya dangane da tarihin daular ta ruman da akan tsakura musu a darasin makarantu. Shugaban masu kula da sashen ya matuƙar nuna jin daɗinsa da bata shawarwari kan tsarin zama mai nazarin tarihi data ambata dan abune daba kasafai ake ganinsa ga matan cikin masarautar ba. Akwai wadda ma bata taɓa taka ƙafarta cikin ɗakin litattafan ba. Amma ita gata ƙaramar yarinya da rayuwarta ke kamar akan ɗar-ɗar abinda ta fara nuna sha'awa na farko akansa kenan. Shine ya fara zaɓa mata books daya ga ya dace ta fara dubawa, hakan yasa ta basar da waɗanda ta shigo nema kai tsaye, dan a ganinta bin shawarar tasa zaifi bata fiye da abinda take buƙata ɗin. Shugaban da shekaru sunyi matuƙar ja a garesa yaji daɗin amsar shawarar tasa da tayi, dan yasan duk da zai iya haifarta matsayinta ya bata ikon yin duk yanda taso a sama da shi... A cikin farin cikin daya goge duk wani damuwarta a wannan yini ta fito hadimanta na take mata baya ɗauke da ɗirka-ɗirkan littafan da ta ɗebo. A yanzu ɗin ma dai tako ina hadimai faman zubewa suke domin girmamawa a gareta harta isa sashenta data basu umarnin su kaita saɓanin sashen Shahan-shan daya kamata ace ta koma tunda a ƙa'ida sati guda zatayi kamar yanda Malikat Haseena ta sanar da Tajwar Eshaan. Iffah kam da ba zama akai aka faɗa mata komai na ƙa'idojin ba haka kawai taji bata bukatar komawa zaman takura da zuciyarta ta ayyana mata rashin amfaninsa. Shi dai wanda aka kaita dominsa ko kallo bata ishesa ba, hasalima baya kallonta da suffar da suka miƙata garesan kai tsaye. Yo dole ta faɗi haka, tunda wane mijin ƙwarai ne zai jefama matarsa kalmar tambaya ta ita (wacece?) Bayan da saninsa aka kai sadakinsa domin aurota. Bazata iya ɗaukar waɗan nan abubuwan ba, dan bama abinda ya kawota nan ɗin ba kenan tun fil'azal. A ganinta kuma ba sai dole an kaita garesa an ƙaskantar da ita ba, zatabi hanyoyin daya dace na haɗuwa da shi har lokacin da zata cika ɓoyayyen burinta.... Da wannan tunanin suka ƙarasa sabon sashen nata. Tabbas ta jinjinama ƙoƙarin su, dan ko makaho ya laluba yasan wannan sashen yayma wanda aka kaita fintinkau a komai duk da shima wancan ɗin dai ba baya bane a tsaruwar. Ta ɗan sauke numfashi da kaiwa zaune bisa ɗaya daga cikin lumbutsa-lumbutsan kujerun da aka shirya falon da su bakinta ɗauke da bismillah. Suma dai hadiman nata bayan sun ajiye litattafan a saman Centre table a gabanta suka zube. Taja tsahon mintuna goma tana mai nazarinsu kafin ta ɗan sauke numfashi da miƙewa. “Ina buƙatar zama da duk wanda zai kasance da Ni a wannan sashen zuwa anjima”. Cike da girmamawa duk suka amsa mata kawunansu a ƙasa. Ta ƙara jan numfashi ta fesar batare data farga da salon izzar da yay kutse ga al'amarin ta na yanzu ba ta kai dubanta ga agogon falon. “Muna da sauran lokaci yanzu da zai ishemu zagaya sashen kafin na shige salla”. Anan ma sun amsa mata ɗinne da girmamawa. Batare da ta sake cewa komai ba tai gaba duk suka miƙe suna take mata baya. A yanzu ma dai wadda ta jagorancesu zuwa books room ce ke mata bayanin sashen da tsarinsa yanda ya kamata. Cike da gamsuwa batare data furta komai ba koda so ɗaya take gyaɗa mata kai. Sashen ya ƙunsa abubuwa masu yawa da zaman lissafinsa zai zama ɓata lokaci da cinye mana page, bayan sun kammala zaga ko'ina Iffah ta shiga bedroom ɗin da zuciyarta tafi aminta da shi matsayin master bedroom ɗin ta. Mamaki ya kamata lokacin da taci karo da guntuwar takarda a saman duvet ɗin saman gadon. _Ibnati wannan ɗakin ki tabbar ya kasance ɗakin sirrinki, shiyyasa nasa a shirya miji duk wani abu na buƙatar ki._ takardar ta ɗan juya tana mai jan numfashi da fesarwa. Sai kuma ta saki murmushi dan ta fahimci saƙon na Daneen Ammarah ne. Wayarta ta ɗauka a ɗan gaggauce ta aika mata saƙo. Sannan ta nufi bayi gabatar da al'wala....... *_★★SHAHAN-SHAN★★_* Tun bayan faruwar komai daya shige ɗaya daga cikin ɗakunan barcinsa bai sake fitowa ba sai yanzu a cikin shirin zuwa Masallaci. Sau ɗaya ya ɗagama hadiman dake zube ƙasa a dalilin fitowarsa hannu ya fice. Da kallon ƙasan ido duk suka bisa, kowa da abinda zuciyarsa ke ayyana masa game da shi... Bayan idar da sallar isha'i bai samu damar shigowa ba yay zaman ganawa da Aamin sa su biyu da suka buƙaci hakan. (Miran Jasim da Miran Arshaan). Miran Arshaan shi yafi jansa a jiki tun fil'azal, sannan kuma kamar yafi kusanci garesa ta bangarorin biyu kasancewarsa miji ga Khaalti (Aunt) ɗinsa da yake kallo tamkar yaya. Shima dai Miran Jasim ɗin bai taɓa nuna masa wani abu mara kyau ba a zahirin rayuwa, a komai ma da zai taso yakan bada ƙarfinsa wajen karesu ne ga kowa koda a fada ne. Waɗannan hallayya tasu ya sashi ɗaukar yarda ya basu har yakan iya tattauna wasu abubuwa da suka shafi mulkinsa, sai dai abinda duk ya shafesa a karan kansa duk yanda zasu so sani baya taɓa basu fuskar hakan dan ko'a zahiri kowa na masa kallon mutum mai wuyar sha'ani, bahagon mai bauɗaɗɗen hali da zurfin ciki ne. Bayan ficewar hadimin daya gama hidimar zuba shayi a gaban kowannensu ya fice Miran Jasim ya fara katse shirun dan yasan in zasu kwashe awa ɗaya a wajen Tajwar Eshaan bazai sake tofa komai ba bayan gaisuwar da yay musu. “Abni nasan zakai mamakin wannan zaman namu, sai dai a dubi da abinda ya faru ɗazun ba abin mamaki bane. Abinda ya faru ɗazun ya matuƙar Kona mana zuciya, dan bazamu taɓa so a aibantaka ba muna ji muna gani kodan amanar da Haysam Akhi ya barmana taka. Akwai wasu abubuwan da yawa daya kamata dama mu tattauna da kai kafin wannan ɗin, amma a yanzu kamar wannan ɗin ne importent”. “Hakane Jasim Akhi”. Miran Arshaan ya karɓe fuskarsa na nuna tsantsar damuwa. Ya cigaba da faɗin, Abni lokaci yayi da nake ganin ya dace wasu a cikin iyayen nan namu dake zaman fadanci ya kamata su huta ƴaƴayensu su karɓesu. Duba da kai matashi ne, a koda yaushe ra'ayinka da hangenka zai cigaba da zama banbanci ne da nasun. Koda yake su a gare sun ma ba haka bane, dan haka mahaifinka yasha gwagwarmaya matuƙa da su a yayin nasa mulkin. Amma kai mi kake gani akan hakan?”. Shiru babu alamar Tajwar Eshaan zai tanka, sai ma cigaba da kurɓar shayinsa yake cike da ƙasaita idanunsa akan television dake aiki a falon..........✍️ *AYYIRIRIRI AHAYYE CHAS 💃🏼💃🏼💃🏼 sunan wata waƙa wai ita LUWAI* _Ana tayi muna tayi manyan mata dai da gaske sun dage sai sun zama kalar gaban mota kalar camera tare da gudummawar Mg's skin care Hajia ta kina ina ake ta wannan harkar arziƙin mata nata glowing suna faranta zuciyar mazajensu da laushi da santsin fatar su ke kina nan kina fama jiki duk kirci😱😱?_ Ah haba madam yunƙuro ayi tafiyar nan dake ki shiga ki wataya acikin shahararrun matan nan da ko'ina ake fatan gani dan an daɗe ana jin su watau *team glow by Mg's* Macen da ta isa itace mace karki bari ki zama cikin irin muna matan nan da suka rako mata duniya kuna tafe da mijinki yana kallon wata har miyau na zuba tsabar haɗuwarta da kyan fatarta Mg's skin care sune sirrin duk wata macen da ta isa a ɗaga kai a kira da suna mace wacce ba'a jin kunyar shiga taro da ita daga nan har villah kizo/kuzo mu haɗe a wannan ƙasaitacciyar tafiyar ta Mg's skin care domin sune na gaban gaba sune suka ciri tuta indai a harkar gyaran skin ce hajiata kiyi wani fresh kiyi smooth wow🥰🥰🥰kina tafe kina walwali idan fa kina amfani da *Mg's skin care* ba kya buƙatar ko wanne irin mai product ɗinmu katt ne duk matsalar fatarki muna da maganinta uhmm inata miki labari nace ba sister shin meye matsalarki ta gaban goshin ƴallaɓai? Acne?, pimples? spot?, strech marks?, sunburn?. to hutas bi'izinilLah muna da maganin matsalarki kina ganin mata a tiktok fuska luwai lumus kice dama ni ko? to in dai kina tare da *Mg's* matsalarki tazo ƙarshe bama cika baki gaskiya itace takenmu haka nan kuma siyen nagari mai da kuɗi gida *MG's skin care gagarabadau* Price ɗinmu daidaitacce ne sannan kuma dai dai da aljihunku *Soap price:4k* maiso yy mgn 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Instagram:glow_with_mgs Facebook: mg's skincare Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki Small 12k Medium 14k Babba 20k *BE PART OF THE GLOW TEAM KARKU BARI A BAKU LABARI* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_38_* ........Duk da yanda zukatansu ke suya da tsagwaron salon wulaƙanci da raini da suke jifansa da shi game da wannan halin nasa da babu komai a cikinsa sai tsantsar miskilanci da kasancewar jinin mulki da ke yawo a jikinsa basu bari fuskokinsu sun nuna ba har ya gama shan ƙamahinsa da basarwarsa ya tanka. “Amfanin kasancewarsu cikinmu yafi rashin amfanin muhimmanci Aam. A lokuta da dama nafi son zama da maƙiyi fiye da masoyi saboda dalilai biyu”. Wani irin kallo suke masa har fuskokinsu na barazanar bayyana sirrin zukatansu. Miran Arshaan yay saurin katsesa da faɗin, “Abni wace irin magana ce wannan? Kakuwa san illar hakan da kakeyi?”. Miran Jasim dake masa kallon gefen ido cikin takaici yake masifa a zuciyarsa. (Shifa wannan wawa ne baima iya jin ƙarshen zance sam). A zahiri kam kallonsa ya sauke ga Tajwar Eshaan da yay biris tamkar bashi ya ɗakko zancen ba. “Ihm kaga Abni ƙarasa, zata iya yuwuwa naka hangen gaskiyar cikinsa rinjaye ne ga namu. Domin kowa da irin yanda UBANGIJI ke fahimtar da shi abu”. Tajwar Eshaan da bai ko motsa ba ga zancen Amin nasa sai da ya shaƙi iska iya buƙatarsa kafin ya ɗan ɗage kafaɗu a yanayin ko'in kula. “Ku manta kawai muje kan magana ta gaba. Wataran zamu ƙarasa wannan ɗin”. Sosai takaici ya maƙure musu maƙoshi su dukansu. Sai dai Miran Jasim har Miran Arshaan yake jin takaici kasancewar shine sanadin katse zancen. Suma shiru sukai kamar bazasuce komai ba a wannan gaɓar. Kafin Miran Jasim ya nisa. “Abu na gaba shine farin cikin tsallakewar matarka. Alhamdullah addu'oin mu sun karɓu, ALLAH yasa ta kasance uwa ga ƴaƴan da zaka haifa masu albarka”. A maimakon amsawa da Amin daga garesa ƙasaitaccen murmushinsa mai ƙara bayyana ƙyawun da ALLAH ya azurtashi da shine ya saki kaɗan yana mai kauda kansa gefe babu alamar zaice wani abu. Suma basu nuna alamar sun damu da sai yace ɗin ba Miran Jasim ya cigaba da faɗin, “Ya kamata a zauna da Tajwar na jihar Hubab da shugaban tsaro akan waccan matsalar itama. Kar muyi sakaci dayin biris da wannan maganar dan bamu san minene manufa ko dalilin faruwar komai ba. Abu mafi ruɗanin shine makamancin haka bai taɓa faruwa a ƙasar ruman ba sai dai muji a wasu ƙasashe har ma mu bada shawara da gudun mawar ganin sun samu zaman lafiya. Idan haka kuma ta fara faruwa a garemu lallai maƙiyanmu na barazana akan nasararmu kenan”. Nan ɗin ma dai kamar bazai tanka ba sai kuma ya dubi Miran Jasim ɗin da alama zancen ya shigesa. “Na baku damar yin duk yanda ya dace Aam”. A take fuskokinsu suka nuna jin daɗin wannan girma daya basu. Sanin halinsa yasa daga haka sukai masa sallama. Har sun miƙe Miran Arshaan yace “Af niko kaga na shafa'a da wannan batun. Abni baka ganin yayi kusa kuwa ace fitar Zawjata-almilk har cikin books room? Yakamata ace tayi haƙurin cigaba da killace kanta kodan maƙiyan da bamu san ta inda suke shirya sabon shiri ba, dan yayi wuri ace mun shagala da tsallakewar ta ta a nawa ɗan hangen. Ai ƙoƙari a tsawata mata ALLAH ya cigaba da kare mana ku ku duka dai”. Miran Jasim ya amsa da Amin yana jinjina kai alamar tabbatar da maganar, sai dai ganin Tajwar Eshaan bashi da alamar cewa wani abu suka fice abinsu. Koda suka fitan ya jima bai motsa a yanda yake ba, da alama dai maganar tasu ta ƙarshe ce ke masa kaikawo. Hasashen kam sai ya zama gaskiya dan akan lips ɗinsa daya motsa kaɗan ya ambaci, “Yarinyar nan ko”. Daga haka ya shanye sauran a cikinsa.... ★★.... ★.... Kamar yanda ta faɗa bayan sallar isha'i ta fito cikin abaya fara tas. Duk da dare ne ƙamshinta da kwarjininta mai ɓoye ƙarancin shekarunta na tare da ita. Fuskarta ɗauke da murmushi mai bayyana haƙora take amsa gaisuwar hadiman da tuni sun kammala taruwa bisa umarninta. Ɗaya bayan ɗaya ta basu damar gabatar mata da kansu da matsayin ayyukansu. Har suka gama batace komai ba tana dai nazarinsu ne. Haka kawai take jin bai kamata ta yarda da kowa ba a wannan gaɓar, dan duk da tausayinsu dake nuƙurƙusar zuciyarta tayi imanin akwai masu gurɓatacciyar zuciya a cikinsu kamar yanda Daneen Ammarah ta karanta mata komai. “Okay duk naji bayanan ku, sai dai kuma Ni zan canja tsarin aikin da bama kowa abinda nake ganin zai fi dacewa da kasancewar tare da ni. Bazan roƙi kowa ba a cikinku cewar ya kasance mai gaskiya da riƙe amana, sai dai zan tabbatar muku zan iya hukunci ga kowa idan na kamashi da waɗan nan abubuwan biyu. Dan na matuƙar tsanar mai wannan halayar koda a sama dani yake. Zan kuma iya aikata harma abinda mutum baiyi zatoba akan hakan.....” ɗaya bayan ɗaya ta rarrabasu ga ayyukan saɓanin yanda aka turosu suyi, salon nata ya matuƙar girgizasu a take kuma tasirin gizagonta ya shigesu, har suke ambaton tsarin da gaba kura baya sayaƙi kenan, dan kuwa dai kamar yanda Iffah tai hasashe mafiya yawan cikinsu zasu kasance da itane bisa umarnin iyayen gidansu na ɓoye bisa ɗabi'ar tura ƴan leƙen asiri da manyan masarautar suka tasirantu a kansa. Bayan ta sallamesu akan aikinsu zai fara daga gobe ne ta tattare littafanta da kanta tai ciki da su. Sai da ta tabbatar ta ƙarema ɗakin kallo yanda ya kamata fiye da ɗazu bisa zargin za'a iya saka mata camara kamar yanda Ajmaal ya tabbar mata. Babu alamar akwai abinda take zargin dan haka ta ɗauka wayarta. A maimakon WhatsApp yau a text message ta tura masa saƙo, daga ƙarshe ta ƙara roƙonsa bincika mata lafiyar iyayenta dan zuwa yanzu zuciyarta na tabbatar mata akwai abinda Sir Fawzan ya faɗa mata ba dai-dai ba ko yake ɓoye mata. Dan kullum takan gwada number Hanash da Babiy sama da sau babu adadi amma babu alamar zata samesu. Ga mafarkinta a kansu duk kusan bayan kwana biyu cikin maimaita kansa yake gareta. Bawai tayi imani da hakan bane, kawai dai zuciyarta takan rinjayu da tsoro akan mafarki musamman idan ta auna da abubuwan da suka tabbata akan wasu mafarkai da sukai wa riƙon wasarere ita da iyayenta a baya....... *_★MALIKAT HASEENAT★_* Kamar yanda labarin fitar Iffah yaje kunnen kowa a masarautar itama yaje nata kunnen, sai dai saɓanin malikat Bushirat ita murmushi tayi batare data furta komai ba akan zancen. Rashin cewar tata ya Bama Hadimar damar ƙarasa mata zancen akan Iffah kuma ta koma sashenta bayan barowarta books room. Anan kam idanu Malikat Haseenat ta tsurama hadimar Tata tamkar zataga fuskar Iffah a jikinta ne. Sai kuma ta janye da wani ɗan murmushi a fuskarta ta maida ga hadima Banou. “A haɗa abincin karin kumallo da Zawjata-almilk ta uku”. Cikin tashin hankalin wannan umarni na Malikat Haseenat kamar Banou zata fasa kuka ta jinjina kai, har hakan ya bama malikat Haseenat mamaki, sai dai batayi magana ba kasancewar tasan shirmen Banou fiye da haka. Itama dai tana zaune da itane batare da tasan dalili ba, amma wasu lokuta takanji yanayi mai wahalar fassara koda a kallon hadimar tata ne amintacciya a bangaren girka mata abinci... 7 *_BARRISTER_* “Su waye ku? Miyasa kuka kawoni nan? Mina muku?”. Barrister ya faɗa yana mai bin zaratan samarin da kallo harma da ɗakin da suka kawoshi mai ƙarancin haske gashi a ɗaɗɗaure a kujera. Fahimtar bazasu bashi amsa ko ɗaya ba daya bukata ya sashi cigaba da magana a hasale. Dan shi mutum ne mai saurin fushi musamman akan gaskiya da mai gaskiya. Baya son zalunci shiyyasa ko baka da ƙarfi zai tsaya maka akan haƙƙinka in har ka kasance mai gaskiya. “Idan ma akan case ɗin nan ne kuke ganin sakayeni ko ɓadda rayuwata zai baku damar yin yanda kuke so akan bayin ALLAH da basujiba basu gani ba ku sani ni bamai hukunci bane. ALLAH shine mai hukunta kowa, zai kuma iya kawo wanda ya fini ƙarfi ya cece su”. Yanzu ɗinma dai babu alamar wani a cikinsu zai tanka masa. Idanunsa ya rumtse zuciyarsa na masa ƙuna. Bashi da wani buri yanzu a duniya sama da yasan asalin tushen wannan case ɗin nasu Babiy, yayi alƙawarin tsayawa da ƙarfinsa dana aljihunsa insha ALLAHU. Har dare babu wani haske daya samu dan har lokacin yana a ɗaure, sai da aka kira sallar magriba ne suka bashi dama yay salla harda isha'i. Hakan ya ɗan sassauta masa zuciya, dan koba komai damar yin salla da suka bashi yaji a ransa masu sassauci ne. Abinci suka kawo masa basu sake ɗauresa ba, sai dai yaƙi yako kallesa hakan yasa suka sake zuwa kusan ƙarfe tara agogon ƙasar suka sake ɗauresa sukai ficewarsu da kullesa ta baya. Babu irin tunani da takaici da baijiba amma ya cigaba da ambaton sunan ALLAH dan yasan shine kaɗai zai kuɓutar da shi a wannan gaɓar. Kusan ƙarfe sha ɗaya gyangyaɗi naɗan kwasarsa yaji ana ƙoƙarin buɗe ƙofar, idanunsa ya buɗe duk da baya iya ganin mai shigowa saboda ƙarancin hasken ɗakin. A ɗan hasken ya fahimci yanzu mutumin uku suka shigo, wanda ke gaba kuma da alama ogansu ne dan yanda ya shigo da takun izza cikin ɗakin. Da sauri suka ajiye masa kujera ya zauna yana mai facing ɗin Barrister yay wani irin zaman ƙasaita yana ƙarema Barrister ɗin kallo ta cikin glasses ɗin daya toshe idanunsa.... “Miyasa kuka dauresa?”. Ya faɗa a kausashe. Kame-kame yaran nasa suka fara kowa na ƙoƙarin kare kansa. Yaja tsakin daya sakasu nutsuwar dole yana mai faɗin, “Ku kwance sa”. Bayan an kwance Barrister ya sake bada umarnin a bashi abinci da ruwa. Barrister dai kallonsa kawai yake da mamakin wannan izza tasa. Baiyi niyyar cin wani abu ba dan haka yay saurin faɗin, “Bana buƙatar wani abinci. Kusanar min kawai dalilin da yasa kuka kawoni nan da kuma inda nake dan ALLAH”. Har Barrister ya fidda rai ga samun amsa yaji an karɓama zancensa a kausashe. “Barrister Abdallah Aas ba shiririta ta kawoni nan ba. Dan na baro abubuwan da suka fika muhimmanci nazo nan. Duk da rayuwarka ce ba sanin inda kake ko sanin mu su wanene ba matsalarka. Dalilin kawoka nan kawai zaka iya sani, damar hakan kuma na hanunka ta hanyar bin umarninmu”. Haka kawai kwarjinin wannan mutum da ko fuskarsa Barrister baya gani da ƙyau yay matuƙar mamayesa, duk da yanaji a ransa ba alkairi yasa suka kawosa nan ba sai yaji bazai iya jayayya da shi ba. Cikin sanyin jiki ya fara cin abincin, yaci kusan lauma bakwai yasha ruwa duk suna a ɗakin. “Na gama”. Ya faɗa cikin sanyin murya. “Good for you”. Aka bashi amsa cikin halin ko'in kula. Sai kuma yay shiru kamar baida abin faɗa kafin yaja numfashi cike da isa ya fesar. “Lokacina ƙurarrene dan haka bani da lokacin cigaba da ɓatashi a rikeka nan. Aiki zakamun baka da kuma zaɓin cewa e ko a'a. Nasan kasan Barrister Akeem Ibn Behnam”. “Hakane, dan abokina ne ma ranka ya daɗe”. Barrister ya amsa mishi da kalmar giramamawa a ƙarshe batare da yasan dalili ba. Kawai dai yana jin matuƙar girman wannan mutum da ko a murya yasan ya girme masa. Cikin yaransa ɗaya ya cigaba da faɗin, “Sanin hakan yasa aikin ya wajaba a kanka. Akwai aikin da Barrister Akeem ɗin keyima wasu mutane, Boss naso ka maye gurbinsa....” “Tayaya hakan zata faru, bayan su sun san wanda suke huɗɗa da shi”. Barrister yay saurin katse mai maganar. “Ai mun fika sanin hakan shiyyasa muka zaɓeka. A yanzu Barrister Akeem na hanunmu kamar yanda kake a hanunmu, munada hanyoyin bi wajen canjaka ka koma shi bisa dalilan da kaima kasani, yayinda su a wajensu kai ka mutu a yanzu, zuri'arka kuma basu san inda kake ba. Zakai aikinne na kwanakin da basu gaza goma ba, idan sun zarta hakan kuma kai kaso”. “Kun sani a duhu wlhy, Barrister Akeem fa wani babban jigone a rayuwata, muna taimakama juna matuƙa taya kuke tunanin zanci amanarsa ta hanyar yin amfani da kammanin da mukeyi ace na masa kutse akan aikinsa bayan haka cin amana ne?”. “Wannan damuwarka ne. Aikinmu zai fara daga gobe”. Ogan nasu ya faɗa cikin kausasa harshe yana miƙewa. “Ranka ya daɗe dan ALLAH ka saurare ni”. Barrister ya faɗa cikin rauni. Sai dai baiko nuna alamar yama jisa ba yay ficewarsa yaransa biye da shi..........✍️ 🤔????. Nama rasa abin faɗa. *AYYIRIRIRI AHAYYE CHAS 💃🏼💃🏼💃🏼 sunan wata waƙa wai ita LUWAI* _Ana tayi muna tayi manyan mata dai da gaske sun dage sai sun zama kalar gaban mota kalar camera tare da gudummawar Mg's skin care Hajia ta kina ina ake ta wannan harkar arziƙin mata nata glowing suna faranta zuciyar mazajensu da laushi da santsin fatar su ke kina nan kina fama jiki duk kirci😱😱?_ Ah haba madam yunƙuro ayi tafiyar nan dake ki shiga ki wataya acikin shahararrun matan nan da ko'ina ake fatan gani dan an daɗe ana jin su watau *team glow by Mg's* Macen da ta isa itace mace karki bari ki zama cikin irin muna matan nan da suka rako mata duniya kuna tafe da mijinki yana kallon wata har miyau na zuba tsabar haɗuwarta da kyan fatarta Mg's skin care sune sirrin duk wata macen da ta isa a ɗaga kai a kira da suna mace wacce ba'a jin kunyar shiga taro da ita daga nan har villah kizo/kuzo mu haɗe a wannan ƙasaitacciyar tafiyar ta Mg's skin care domin sune na gaban gaba sune suka ciri tuta indai a harkar gyaran skin ce hajiata kiyi wani fresh kiyi smooth wow🥰🥰🥰kina tafe kina walwali idan fa kina amfani da *Mg's skin care* ba kya buƙatar ko wanne irin mai product ɗinmu katt ne duk matsalar fatarki muna da maganinta uhmm inata miki labari nace ba sister shin meye matsalarki ta gaban goshin ƴallaɓai? Acne?, pimples? spot?, strech marks?, sunburn?. to hutas bi'izinilLah muna da maganin matsalarki kina ganin mata a tiktok fuska luwai lumus kice dama ni ko? to in dai kina tare da *Mg's* matsalarki tazo ƙarshe bama cika baki gaskiya itace takenmu haka nan kuma siyen nagari mai da kuɗi gida *MG's skin care gagarabadau* Price ɗinmu daidaitacce ne sannan kuma dai dai da aljihunku *Soap price:4k* maiso yy mgn 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Instagram:glow_with_mgs Facebook: mg's skincare Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki Small 12k Medium 14k Babba 20k *BE PART OF THE GLOW TEAM KARKU BARI A BAKU LABARI* *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_39_* ........A ɓangaren Iffah kam bayan sallamar Hadimanta data ƙudiri nutsuwa wajen fahimtarsu a tsanake itama ciki ta shige. Kamar yanda ta saba sai da ta gudanar da duk wani al'adan rayuwarta kafin barci. Ta haye sabon katafaren gadon nata bakinta da addu'a. Manya-manyan littafan dake jere a bideside drawer ɗinta data kwaso a books room ta kalla cikin nazari har idonta ya sauka kan wanda ya kamata ta fara dubawa. Sai da taja lalausan bargon dake a saman gadon ta ɗan rufe kafafunta zuwa cinya ta gyara zamanta da ƙyau ta buɗe littafin da bismillah. A nutse kuma daki-daki ta fara nazartar littafin da ƙoƙarin dinga fahimtarsa yanda ya kamata da irin fahimtar dai-dai nata tunanin. Taja wani tsahon lokaci a nazartar littafin barci gwanin iya sata ya cigaba da rinjayar idanunta. Haka badan taso ba ta kife book ɗin a gefen ta zame ta kwanta tana hamma. Da ƙyar ta kammala haɗa addu'ar barci...... ★★..... ★..... “Uwa komai ya rikicemun wlhy, narasa ina zan kama. Ki taimakeni kar yaƙin dana sha a baya ya zama wahalar banza akan cikar burina”. Ta-kurya ce mai maganar cikin tsananin tashin hankali da susucewa game da rashin mutuwar Iffah kamar na sauran matan baya”. Uwa dake hakimce duk tana saurarenta ta nisa tana mai girgiza kanta da sake tsuke mummunar fuskarta. “Ƴar shilar nan bata isa ja dani ba Ta-kurya, kin Sanni kin san aikina kin kuma san mizan iyayi. Ya kamata ki nutsu tsaf akan bayanin danai miki tun a baya. Tabbas mutuwarta zata iya zame mana mai wahala a lokacin da muke buƙata, shiyyasa naji takaicin suɓucewar waccan damar da muka samu a farko. Gashi kema sakacinki yasa har zuwa yanzu kin gagara kawo mana rigar dake sashen mai Babban ɗaki ko zamu iya kamo bakin wancan zaren dan zuwa yanzu na fahimci akwai masu irin manufarmu akan yarinyar kamar yanda na sanar miki. An kuma mana karan tsaye na kaita sashen Ajlaan ta hanyar ƙin bin dokokin kaita turakarsa, kin san kuma mu munbi matakanne wajen ɗana tarko akan waɗan ca har mukai na sara, sun shammacemu sun kaita ne, sai dai abinda basu sani ba hakan bazai taba tseratar da itaba a tarkonmu na gaba da kuma mutuwarta” “Uwa ba sakaci bane, a yanzu haka hadimar dana saka wannan aikin tana gab da kammala min shi. Ni yanzu tashin hankalina shine cikar lokacin kalmashe bakin zaren burina na biyu dake ƙara nisa. Har yanzu da buƙatar cikamakon aikin fa kafin na tsallaka na uku da shine cikar gaba ɗayan nasarata akan wannan yaƙin. Uwa ya kamata kiyi wani abu. Idan ita wannan yarinyar mutuwar tata bazai yuwu ba ta wannan silar inaga mu ajiye batunta gefe a haɗe wannan bakin zaren”. “Kema kinzo da magana mai ƙyau kam ta ƙurya. Kuma inaganin ya kamata cikin Zawjata-almilk biyu da suka rage ɗaya zata zama cikamakin ayyukanmu na biyu. Kinga sai mu haɗa aikinmu na uku dana ƴar shilar sudan can, amma duk da haka a kwana bakwai da zatai bazamu daina gwada sa'ar mu ba dai”. “Haka shine dai-dai uwa mai share kukan masu kuka. Madubin rayuwar duk wani mai buƙatar kallon ƙarshen ƙyawun nasararsa.” “Nasara takice Ta-kurya tunda har kina tare damu. Sai dai maganar yarinyar can dole ki haɗa da kirsa a yanzu kamar yanda kika saba wajen nasarar haɗa dukkan auren Ajlaan ta hanyar mai Babban ɗaki a yanda kika so. Ki kusanta kanki da yarinyar itama sosai”. “Indai wannan ne angama Uwa”. “Na barki lafiya”. Uwa ta faɗa tana mai ɓacema ganinta a sannu-sannu harta daina ganinta. Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke ranta duk babu daɗi. Dan zuciyarta kam ta fara ayyana mata ƙarfin ikon uwa ya fara sanyi. Dole ne ta nema sabon mai taimakonta duk da bazata taɓa mantawa da gudunmawar da uwa ta bata ba harta kawo wannan matsayin a wannan daula ta ruman da ayanzu take kamar mai juyata ta ƙarƙashin ƙasa da zahiri a yanda take so. Amma ga karamar yarinya da bata wuce kiyashin da take murjewa a ƙasan tsinin takalminta batare data sani ba tana neman zamewa rayuwarta wata ƙadangaren bakin tulu a gabar cikar babban burinta na ƙarshe...... ★★★..... ★★.... ★.... A ɗan firgice Iffah da kiran sallar asubahi ya farkar take kallon kanta da inda take a yanzu. Cikin shiga razani mai ban tsoro ta diro a gadon daya kasance saɓanin inda ta kwanta a daren na jiya. Kamar wadda ake ingizawa ta fice a ɗakin cikin sassarfa. Tabbas sashen Tajwar Eshaan ne dai take. “Taya haka zata kasance?”. Ta faɗa cikin bugun zuciya. Sai kuma ta fara tunanin kodai mafarki take yine. Hannu takai ta ɗan mari fuskarta. Sai dai babu abinda ya canja daga wanda idonta ke gane mata a yanzu. Dan lallai da gaske a sashen Shahan-shan ɗin dai take. “Ya ALLAH mike faruwa da ni ne haka wai. Taya zan kwanta a sashen da ba wannan ba na kuma buɗe ido na gannni? Jiya an ɗaukeni daga ƙasa an maida saman gado na share, amma shine yau kuma za'a ɗakkoni daga wani sashe zuwa wani daban. Anya ba matsafan gidan nan ke son min wasa da hankali na ba?”. Wannan tunani na karshe ya sata saurin kama rigarta ta shinshina. Tabbas irin dai ƙamshin turaren jiya ne da karfinsa harya danne nata. “Ya Arrahaman” ta sake faɗa tana mai juyawa ta shiga kallon ɗakin da sauri. A kan tarin kayan turarruka da idonta ya sauka a kai ta nufa, ta buɗe gilashin da suke ciki kamar dai nacan ɗakin ta fara shinshinasu ɗaya bayan ɗaya. Sai dai abin mamaki babu wanda ƙamshinsa yay kama da wanda takeji a jikinta. (Dole ne ma na gano, kuma ta wannan ƙamshin insha ALLAH). Ta ayyana a zuciyarta cike da alwashin hakan. Alwala taje ta dauro jin makara na neman riskarta. Bayan ta idarne kuma ta sake nutsuwa wajen ƙarema ɗakin kallo yanda ya kamata. sai yanzu ma ta gane ba inda ta kwana a jiya bane wani ne daban. Sai dai shima wannan ɗin ya matuƙar haɗuwa fiye ma da wancan ɗin. Saɓanin wancan da tsarin komai na cikinsa ke fari anan kuwa komai blue ne, ga wani ƙamshi na fitina na tashi kamar dai wancan. Abu mafi ban mamaki nan ɗin dai duk da ya nuna ana tsaftaceshi a hargitse yake kamar anyi dambe a cikinsa. Ita kanta dama a shigarsa toilet har mamakin yanda taga kanta a birkice tai, dan tasan dai tsaf ta kwanta kuma bata buge-buge a barcin. Son yin salla a kan lokaci ya sakata bata maida hankali ba sai yanzu data idar ta samu nutsuwa. Tayi tunanin gyara ɗakin da fita binciken turaren nan na jikinta da alama ya tabbatar mata mai shi ke son wasa da tunaninta, sai dai wata zuciyarta ta bata shawarar ajiye waɗan nan batun ta sake kwanciya irin ta jiya tai likimo kozata samu bakin zaren ta hanyar shigowar wanda take zargin kamar jiya. Ta gamsu da hakan tako kwanta, sai dai tsahon kusan awa ɗaya babu wani wanda ya zo ɗakin, babu ma alamar wani ɗin zai zo harta tashi akan dole ta kimtsa ɗakin ta shiga wanka. Kayan data samu a lokacin gyaran ɗakin ta sanya babu ko ɗar a ranta. Tayi ƙyau sosai, ta kuma sake baza turarurrukansa a jikinta kamar jiya sannan ta fice a sannan kusan ƙarfe bakwai da rabi... Da ƙyar yau ma ta iya gano ɗakin data kwana a shekaran jiya, cikin Sa'a kuma ta samesa a buɗe. Shiga tai da sallama duk da bata zaton samun kowa a ciki. Tsaf yake kamar batai bidiri cikinsa ba jiya, an canja zanin gadon ga kamshi na tashi mai daɗi da sanyin ac. A yanda hadiman suka nuna sun ɗan yi shock da ganinta ya ɗan sakata a mamaki, amma sai ta dake babu alamar hakan gareta ta nufi ɗaya daga cikin kujerun falon tai zaman ƙasaita da ita kanta bata farga da yinsa. Hadiman da duk ganinta ya sakasu a firgici suka iso gabanta suka zube domin miƙa gaisuwa. Rayukansu kam cike da mamaki dan kowa dai yasan a jiya ba sashen ta kwana ba, tun fitar yamma da tai bata sake dawowa ba har suka rufe waje suka kwanta. Tun bayan idar da salla asuba kuma suka fito balle suce koda safen nan ta dawo. A fisge ta amsa gaisuwarsu tana mai sauke manyan fararen idanunta akan ƙyaƙyƙywan tray ɗin dake ajiye a table ɗin gaban kujerar data zauna a jiya wadda koda ba'a faɗa mata matsayin kujerar ba tasan ta zaman Shahan-shan ce. Ɗan juyiwa tai ta dubi hadiman da har sun fara miƙewa. Ta jeho musu tambaya da faɗin, “Wannan fa?”. Cikin sauri mai sanye da kayan kuku ta amsa da “Shayi na farko da Shugaba ke sha bayan gama motsa jiki”... “Kayan haɗin sa?”. Ta tambaya a takaice. Nanma da tsumar jiki ta lissafa mata. Iffah ta yamutsa fuska da sake harɗe ƙafafu. “A canja minsu da tatattun kayan itatuwa da ganyen koren shayi”. Cikin tsoro duk suka dubeta, ta sake tsuke fuska da musu alamar gargaɗi da hannunta. Kamar ƙyaftawar ido kukun ta ɓace a wajen. Cikin abinda bai fi mintuna goma sha biyu ba aka dawo da wani sabon haɗin shayin. Miƙewa Iffah tai da nuna hanya alamar ta kaita inda yake. Anan ma ba karamin tsoro bane ya bayyana a idanun hadimar har ma da sauran ƴan uwanta, amma tsayayyun idanunta masu ƙarfi fiye da girman shekarunta ya hana hadimar iya furtawa a baki. Kai tsaye hanyar dake acan gefe ta nufa, sai dai suna zuwa ta dubi Iffah a mariraice sai kuma ta duƙar da kai. “Tsahon rai da amincin UBANGIJI su zama kariya ga Zawjata-almilk, wlhy bani da hurumin tsallake wannan iyakar”. (Kinyi mai wuyar) cewar Iffah a zuciya. A zahiri kam hannu ta miƙa ta amshi tray ɗin batare da tace uffan ba. Cikin rawar jiki hadimar ta buɗe mata ƙofar gilashin dake a wajen, Iffah ta ɗan tsirama steps na bene daya bayyana alamar shi zatabi kusan na sakan ashirin kafin ta maida ga hadimar da kanta ke duƙe, “Zaki iya komawa bakin aikinki”. Kamar dama umarnin take jira, cike da sassarfa tabar wajen ƙwaƙwalwarta fal mamakin wannan baiwa har zufa na taruwa a goshinta. ★Ba karamin sake jinjinama al'amarin wannan masarauta Iffah tai ba, dan tana ɗaura kafarta a step na farko na'ura ta fara shelanta kasancewarta a wajen. Abu mafi bata mamakin kalmar sunan da na'urar ta ambaceta da shi. Kafin ta sami damar wani waige-waige lifter data kwasota ta direta a wata ƙofar da hadimai biyu ke tsaye hannunsu riƙe da manyan bindugu. Tayi mamakin ganin yanda suka rissinar da kawuna sunka fara gaisheta. (Shin sun yarda da zancen na'urar ne? Kokuwa sun santa a matsayin Zawjata-almilk ɗin ne dama?). Da wannan tambayar da babu mai bata amsa ta cigaba da takawa a hankali kasancewar sun buɗe mata ƙofar wajen. Iska mai daɗi dake busawa ta sanyin safiya ta fara cin karo, ta zuƙa a hankali tana mai lumshe idanunta. Sai kuma ta buɗesu a sannu, a lokaci ɗaya bugawar zuciya da tsinkewar jini suka nema sarƙe numfashinta, neman daburcewa take sakamakon abinda tai tozali da shi. Babu shiri ta maida idanunta ta rumtse tana mai ambaton sunan ALLAH akan wannan mummunan gani da tai. To mummunan gani mana, dan tunda take a rayuwarta bata taɓa tozali da namiji a irin wannan yanayin da idonta ya gane mata ba.. Ji take kawai ta zura da gudu ta koma, sai dai hadiman dake bayanta fa? Wane irin kallo zasu mata bayan na'ura ta gama fallasata a garesu. Tabbas nuna gazawarta na nufin faɗuwarta, faɗuwarta a matakin farko kuwa na nufin rushewar gaba ɗaya nasararta. Da karfi taja numfashi mai kauri ta haɗiye, kamar zatai kuka ta sake buɗe idanun a hankali, sai dai koda wasa bata yarda ta kalla gaban nata ba..... Shigar ƙamshin turarensa da bayan shi babu wani mai irinsa da sautin takun takalman ƙafarta ya sashi juya sharɓeɓen takobin dake a hanunsa cike da gwanancewa ya karci ƙasa ya gocema Aamin nasa da suke wasan tare ya juyashi zuwa hannunsa na haggu saɓanin na dama sai gashi akan wuyan Iffah da numfashinta yay wata irin mummunan fisga. “Who are yo.....?”. Yay yunƙurin faɗa cikin alamun bayyanar fushi mai haɗi da isa da ƙasaita, sai dai kalmar ta gagara ƙarasa fita a harshen nasa dalilin tozali da abinda bashi yay tsammanin gani ba. Tar-tar fuskokinsu suka bayyana akan takobin mai matuƙar ƙyalli da sheƙi da kai tsaye za'a iya kiranta faɗama jini na wuce........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_40_* ..........Tsam Iffah ta ƙara damƙe trayn hanunta jin rawar jikinta na neman fitowa, “Barka da safiya ranka ya daɗe”. Ta faɗa cikin ƙarfin hali da jarumtar saka idanunta cikin tsakkiyar nasa da ke tsaye a kanta har yanzu ƙyam. Sai dai duk ƙwaƙwƙwafin mutum bazai iya gane abinda ke a cikinsu ba balle akan fuskarsa mai cike da gizago akoda yaushe. Ganin bai amsa ba, bai kuma daina kallon tsakkiyar idanunta da ayanzu take ƙoƙarin janyewa a nasa ba, bai kuma janye takobin da kallonta kawai zai iya tada tsigar jikin mutum daga wuyanta ba ya sata ɗan shammatarsa ta goce makoshinta da ga tsinin takobin daya ɗaura matan, sai dai a yanda ya wani lumshe idanu da sauke takobin yasata tabbatar da ya bartane kawai. Gaba tai yunƙurin yi, da yima hadiman da suka iso wajen yanzu nan kallon gefen ido a kaikaice ta saki wani lallausan murmushi mai ma'anoni da yawa a zahiri. A kuma ƙasan ranta ko ɗar babu. Duk wannan abun Miran Arshaan fa na tsaye a wajen ne yana ƙarema Iffah kallo a kaikaice cike da mamakin ƙarfin halin yarinyar, dan tunda yake a wannan masarauta bayan shi babu wani mahaluki daya taɓa zuwa wannan wajen sai Shahan-shan da hadiman dake kula da wajen. Amma a yau sai ga yarinya ƙarama da babu alamar tsoro a cikin idanunta a wajen. Sai kuma yanda tayi kamar bata gansa ba yay matuƙar ƙona masa rai amma ya dake dan yana buƙatar ganin ƙarshen wasan.... Wajen duk da filine na karshen ginin (rufinsa kenan) ya ƙawatu da abubuwa kashi-kashi na more rayuwa. Ga wani ƙamashin furanni da aka ƙawata waje dana fresh air masu narkar da jinin mutum da sanya kasala. Da sauri ɗaya daga cikin hadiman da suka shigo wajen da abubuwa a hanunsu ya ƙarasa ga Tajwar Eshaan dake murza goshinsa kansa a ɗan rissine ƙasa. A gabansa ya dirƙushe yana mai miƙa masa kufan takobin hanunsa da babu tantama anyi adon jikinsa da gold ne. Takobin ya ɗaura masa kan dogon trayn da kufan yake. Hadimin ya miƙe da sauri yana ja da baya. Na biyu ya iso da sauri shima, sai dai saɓanin na farko shi bayansa ya koma yana warware farar rigar hanunsa mai maɗauri. Hannayensa ya ware da ɗan kai idanunsa inda Iffah ke tsaye tana tsiyaya shayi a karamin kofi, ya wani irin ɗage kafaɗu da juya rigar cike da salo ta rufe jikinsa tare da zarge igiyoyin biyu akan damammen cikinsa. Hadimi na uku ya iso shima ya durƙushe hanunsa dauke da ƙaramin farin towel. Nan ma dai ɗauka yay ya rataya a kafaɗa bayan ya ɗan tsane zufan daya taru masa a gefen wuya da goshi alamar dai jininsa a tsinke yake a lokacin. A yanda hadiman suka sani daga haka hanyar da zata maidashi bedroom ɗin daya kwana yake bi, acan zai samu shayinsa na ƙa'ida mai dafawa ta kai, bayan yasha zai shiga wanka kafin ya fito inda aka shirya masa karin kummalo. Sai dai saɓanin yau yana ɗaga ƙafa domin barin wajen bayan ya dubi Aamin nasa ya rissinar da kai kaɗan na alamar sallama da girmamawa a garesa Iffah dake faman baza ƙamshin da ga Shahan-shan ɗin kawai suka sansa ta isowa wajen ɗauke da ƙaramin kofin shayi dake tururi fari tar na glass. Da sauri duk hadiman suka juya bayansu, dan kallon abinda zai iya biyo bayan wanda suka gani ɗin haramunne a garesu. Iffah dake taku a nutse kamar wata hawainiya takalmanta da ba wani tsinin kirkine da su ba na bada sautin isar da saƙon tahowar tata ta iso gabansa.. Ƙin yarda tai koda wasa su haɗa idanu. Idanunsa da kallonsu ke canjawa ya sauke akan kofin shayin da take miƙo masan. Shiru babu alamar zai amsa, har hanunta na ƙoƙarin fara yin dayi. Sai da ta fara ambatar sunan ALLAH kafin ta ɗago fuskarta a dake, “Ƙin sha na nufin rauni da muhimmancin Zawjata-almilk a gareka. Ko kuwa cigaba da tabbatarma duniya abinda suka sani shine gaskiya ranka ya daɗe”. Yanda lips ɗinta da suka sha pink lipstick ke motsawa ya zubama ido, sai dai maimakon mata sharhi akan zancenta kamar yanda taso yau gefe ya ɗan maida kansa da amsar shayin kamar wanda ya shiga halin tarkon kasala. Karan farko ta sakar masa wani lallausan murmushi da faɗin, “Thanks”. Basarwa yay ta hanyar ɗan duban gefensa a takaice ya furta, “Aami”. Da sauri Iffah ta duba wajen tamkar sai yanzu ne taga Miran Arshaan ɗin, “Ya salam”. Ta faɗa a zahiri da nufarsa ta zube ƙasa domin miƙa gaisuwa a garesa. Ya ɗan murmusa zuciyarsa taf da al'ajabin wannan figigiyar yarinya da da auren wuri yayi ya haifa wanda suka fita nesa ba kusa ba. Cike da salonsa na fuska biyu ya amsa yana mai ƙare mata kallo ta ƙasan ido. Iffah daba kula da hakan tai ba cike da girmamawa ta miƙe da faɗin, “Uncle bara a baka shayin kaima”. “Zan so kasanwa na farko da zai ci abu daga hanunki Ibnati”. Jin daɗin kalamansa yasa Iffah sakin murmushi da ɗan rissinawa ta furta, “Na gode Aam”. Shima dai shayin ta kawo masa, nan ma yay mata godiya da sanya albarka yana ɗan duban sashen da Tajwar yake tsaye dafe da ƙarfen da aka zagaye wajen ta bakin ginin yake ya tsurama cikin masarautar idanu yana ɗan kai shayin bakinsa tamkar bai san abinda ke gudana a wajen ba. A hankali ya taka inda yake shima yana shan nasa. “Yanzu ne daular ruman ta tabbatar da samuwar Zawjata-almilk”. Sarai Tajwar Eshaan ya jisa. Amma halinsa na ƙasaita da mafi yawan iyayen nasa suke ambato da girman kai yasa yay tamkar baiji ɗin ba. Sai ma juyawa da yay bayan wasu sakkani ya dubi Aamin nasa cikin tausasashiyar muryarsa mara hayaniya da kamewa ya furta. “A huta gajiya”. Ya bar wajen. Ga mamakin duk wanda ke'a wajen gaban Iffah dake ɗan nisa da su ya isa. A bazata taji tattausan tafin hanunsa da yay sanyi ƙalau sakamakon iskar wajen a cikin nata. Da sauri ta rumtse idanu tana mai ambaton sunan ALLAH a zuciyarta da ɗan dubamsa. Ba ita yake kallo ba, sai ma fara takawar da yay wanda ya tilastata binsa tamkar raƙumi da akala. Batare da sun luraba takun sawayensu na sauka da ɗagawa a tare sakamakon shima tafiyar izza da ƙasaita irin na masu mulki yasa baida garaje a tafiya tamkar wani mace. Anan ɗin ma dai tana sanya ƙafarta na'ura ta sanar da ita wacece, haka shima. Da sauri hadimin dake a ƙofar ya zube yana kwasar gaisuwa. Hannu kawai ya ɗaga masa yay gaba abinsa har lokacin hannunsa na cikin nata ya riƙe gam kamar wanda aka bama amanar riƙon nata dan karta suɓuce...... ★★..... ★★...... A ɓangaren Barrister kamar yanda mutanen can suka sanar masa hakance ta faru. Sunyi amfani da kamannin da mutane suka daɗe da sanin sunayi, wanda shine ma tushen zamowarsu abokai, aikinsu kuma ya maidasu aminai. Sai dai muryarsu ta banbanta da wasu abubuwa na ɗi'ar yau da kullum. Akan wannan ne mutanen suka bashi training na dole dalilin barazana da sukai masa akan iyalinsa dama kashe Barrister Akeem ɗin da yake gudun cin amana. Bayan kimtsawarsa da shiga irin ta Barrister Akeem da bashi wasu bayanai akan aikin da zai musun suka bashi key ɗin motar Barrister Akeem. Sun sanar masa dukkan motsinsa akan idonsu ne, kuskure ɗaya akan ganganci fansar rayuwar ɗaya daga cikin ahalinsa ne kona Barrister Akeem. Dole Barrister ya kwantar da hankalinsa dan ya fahimci mutanen sunfi ƙarfinsa, gashi koba komai yana buƙatar kuɓuta kodan tarin ayyukan dake gabansa musamman akan aikin da ayanzu ya tasa a gaba da alƙawarin cika alƙawari. Su da kansu suka bashi address ɗin inda zaije, yayinda ya hau titi kuma sai ya fahimci suna biye da shi a mashina wasu a mota. Ya ɗan rumtse idanu da jan kakkauran numfashi ya fesar lokacin da ya gama dai-daita parking a inda suka umarcesa zuwa. Sai da ya karanto addu'ar neman ɗauki ga ALLAH sannan ya fito riƙe da brefcase ɗin Barrister Akeem a hannu. Ƙaton gidan ya ɗan ƙarema kallo kafin ya nufi inda suke sanar masa yabi ta hanyar bluetooth ɗin kunnensa. Kansa kawai yaɗan gyaɗa tamkar yana gabansu ya nufi ƙofar...... ★★★....... ★★..... A cikin masarauta kam kusan ƙarfe tara da wasu mintuna labari mai razanarwa na rashin ganin Sayeed Khairul-Bashar (Aami gasu Miran Arshaan. Kaka kuma ga Tajwar Eshaan. Shine wanda yay maganar jiya a ɗakin tattaunawa bayan tashin Tajwar Eshaan). Zancen rashin ganin nasa ya fito ne daga iyalansa, da farko an ɗauka yana cikin masarautar ne dan sun tabbatar daga sallar asuba bai dawo ba. Amma ganin har lokacin shigarsa gida ya wuce ƴaƴansa kuma sun bincika a inda suke tunanin ganinsa amma babu shi sai suka fitar da maganar. A take sojojin gidan masu bada tsaro dama hadimai suka bazu lungu da saƙo amma babu alamar hakan. Anbi diddigin wasu daga cikin cctv footage amma fitowarsa kawai aka gani daga sashen nasa babu komawarsa. Hakan ya matuƙar bama kowa mamaki da ɗaure kai. Dan ta ko'ina masu tsaron ƙofofi sun tabbatar basuga fitarsaba sukam. Gashi kuma an duba lungu da saƙo na gidan amma babu wata alamarsa..... ★★...... Lokacin da labarin rashin ganin Sayeed Khairul-Bashar ya iso kunnen Miran Jasim da Miran Arshaan dake tare kallon juna sukai, sai kuma duk suka kauda kawuna suna murmushi. Cikin son basar da zancen Miran Jasim ya cigaba da magana kan zancen da Miran Arshaan ya kawo masa dangane da Iffah “Lallai wannan yarinyar hatsabibiya ce, aini tun isowar labarin kasancewarta raye a safiyar jiya al'amarin ta kemun kai kawo. Zancen ka na yanzu kuma ya sake tabbatar min da shirinta ta shigo masarautar nan.” “To ai ta tara ta samu, dan dama mu irinta muke nema”. Cewar Miran Arshaan yana ɗan murmushi. Miran Jasim ya jinjina kai shima yana murmushin nasa na izza da ƙasaita. “Hakane kam ta kawo kanta inda ake jirace da zuwanta. Dan kam zamu sauke ƙuruciyar dake izata a tunanin yin rawa da bazarta dake ɗawainiya da ita. Zata ƙarasa mana aikinmu cikin sauƙi batare da ita kanta tasan a cikin tarko take ba”. Nan ma murmushi Miran Arshaan yay idonsa akan ɗan uwan nasa. “Zuwa yaushe aikinmu zai fara?”. Miran Jasim ya ɗan ɗage kafaɗa da taɓe baki. “Bazai ɗauka lokaci ba. Sai dai muna bukatar wani point ne dole”. “Wanda yake hannunmu fa?”. Cewar Miran Arshaan da mamaki. “Kai wannan bashi da wani ƙarfin da zaiyi tasiri ita a gareta, duk da dai zai iya zama kamar share mana fage ne. Zaren da nake ganin zamu ja ya kaimu gareta ɗaya ne, duk da dai har yanzu babu wani shaida dangane da tsallakewarta itama. Amma zamu yi amfani da damar, a wannan karonma matarka ce zata mana aikin”. “A wannan gaɓar fa ya kamata mu canja salo, Jasrah nada matuƙar wayo, kar yawan bugar cikinta fa yasa ta fara fahimtar wani abu”. “Sai idan kaine ka bada ƙofar hakan Arshaan. Shekara nawa muna amfani da itan bata fahimtaba sai yanzu. Ka dai kawai ka kasance mai lura”. Kai kawai Miran Arshaan ya jinjina batare daya ce komai ba...... ★★★...... Suna yin ɗan nesa kaɗan da masu tsaron ƙofar Iffah ta zare hannunta da sauri tana ɓata fuska. Bai ko juyo ya kalleta ba balle ya nuna alamar yasan mitayi yay gaba abinsa cikin takunsa na nutsuwa da tsantsar ƙasaita tamkar baya son taka kafafun nasa. Da ƴar hararar ƙasan ido ta bisa tana ƙunƙuni a zuciyarta. (A haka dai kamar na wani limamin masallacin Saudiyya, sai dai zuciyar ko kafiran farkon ƙarni haka suka gansa suka barsa. Wanda duk zai iya salwantar da rai yay barci lafiya babu ko ɗar ai ya dace ka kirasa da duk sunan daya zo maka a rai dan ya cancanci haka). “Ni zanyi maganinka da izinin ALLAH”. Ta faɗa a zahiri fuskarta na nuna gaskiyar ɗacin da zuciyarta ke mata.......✍️ 🥱Bazamu hanaki ba Iffahn mu🏇😉. *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_41_* .......Shiru yay yana kallon inda ya saba iske shayinsa, wayam babu komai, ya kai zaune a kujerar cikin alamun gajiyawa, a gefe kuma tsaurin idon yarinyar da ƙarfin halinta na masa kaikawo. Shan wannan shayin ya zame masa jiki da in bai sha ɗin ba sam bama yajin daɗi, har ma yakan tsinta kansa a wani yanayi da shi kaɗai ya barma kansa matsayin sirri duk da abun na matuƙar damunsa. Har yayi yunƙurin dauriyar sharewa tunda ya ɗan sha wani amma jin abinda yake gudun na taso masa ya sashi furzar da zazzafar iska, babu shiri ya danna alerm ɗin dake isar da saƙon kira ga amintattun hadimansa. Cikin mintunan da basu wuce uku ba ko sai ga ɗaya daga cikin su ya iso. A gabansa ya zube cikin tsumar jiki yana mai ambaton... “ALLAH ya ƙara ma Shugabana tsahon rai da ingantacciyar lafiya, umarninka shine abin jirana”. A zuciya ya amsa da Amin, a zahiri kam babu alamar zai tanka kamarma bashi ya bukaci ganin hadimin ba. Tsahon mintuna uku ƙasaita da izza irinta saraki na dawainiya da shi kafin ya motsa lips ɗinsa a hankali cikin bada umarni. “Miya hana a kawo shayi?”. Hadimin ya ƙara ƙasa da kai jikinsa na ɗan rawa. “Umarni ne daga Zawjata-almilk”. (Umarni?!) Ya maimaita kalmar a zuciyarsa cikin ƙara ƙanƙance idanunsa. (Shi kam ya zaiyi da yarinyar nan ne? Mai kama da alja.....) Ya sake ayyanawa a zuciyarsa batare da ya ƙarasa ba. Sai kuma ya kalla hadimin ya ɗauke kai. “Ina buƙatar waninsa”. Da sauri hadimin ya ƙara gurfana yana amsa masa ransa fal mamaki da al'ajabin wannan sabon al'amari. Fuskarsa gwanace wajen shanye sirrin dake bayyane, amma yanda ya yatsinata da lumshe idanu a yanzu zai tabbatar maka akwai magana tattare da shi..... ★★ Duk yanda taso nuna halin ko'in kula kan abinda ya farun yanzu hakan ya gagara. Dan mayataccen ƙamshin turarensa daya bambanta da wanda ta saka duk da suma nasa ɗinne ya mugun addabarta. Takai hanunta kan hanci yafi sau biyar, sai ta shinshina sai kuma ta janye tana laɓe baki. Hakan kuma bai hana anjima ta sake maidawar ta shinshina. Daga ƙarshe da taga abin na neman zama mata ɗan kaɗafi sai ta faɗa toilet ta wanke hanun da sabulu, amma dan mayata yaƙi ya daina sai da ta ɗauka ɗaya a cikin turarrukan datai amfani da su na ɗakin tasa a hannun sannan ta daina ji. Littafinta ta ɗauka domin cigaba da nazari, sai kuma ta tsaya cak, wani tunani ne yazo mata a zuciya, dan haka ta miƙe zaraf tana ɗaukar wayarta data gani tare da littafin alamar duk ma wanda ya kawota tare da su ya kawotan. Kamar yanda ta saba idan zasuyi magana tai dawnlording sabon WhatsApp app, sai da ta daidaita komai sannan ta lalubosa. Baya online gashi kuma tana buƙatar yau suyi magana ne bawai saƙo take son ajiye masa ba. Sai hakan ya sata jin babu daɗi har walwalarta ta ɓace. “Kona masa flashing?”. Ta faɗa cikin sigar tambayar kanta. Kan ta daga alamar gamsuwa, ta fito a watsap ɗin. A karo na farko tai dailing number ɗin cikin shakku. Harta katse ba'a ɗaga ba, damuwarta ta kara bayyana. Harta sake komawa watsap ɗin ta fito ta sake danna kiran. A hankali ta sauke ajiyar zuciya har ana iya jinta daga can. Tai sallama cikin yar muryarta dake nuna zumuɗin jin an ɗaga, sai dai ba'a amsa mata ba gashi kuma tanajin alamar ana saurarenta. Danne takaicinta tai ta sake sallamar, nan ma shiru dai babu ma alamar za'a amsa. Cikin suɓutar baki taja tsoki da faɗin. “Nifa a rayuwa na tsani walakanci wlhy, shiyyasa komai nafi yarda naima kaina. Yanzu haka wani ɗan iyan dake ƙarƙashin sa ya ɗaga kiran kamar waccan ranar dana fara kira, ƴan hana ruwa gudu kenan. Nima badan ƙaddarar faɗawa hannun wannan Dodon ba da yanzu ina can ina karatuna na jaridar a daina yarfani. Kai insha ALLAHU kafin naga bayan a azzalumin nan ko sau ɗaya ne sai na hau kujerar karagar mulkin nan nayi tankaɗe da rairaya cikin duk ƴan jaridar ƙasar nan da jami'an tsaro aikin banza......” Jin kamar sautin fitar murmushi a kunenta ya sata saurin ciro wayar ta kalla. Dai-dai ana yanke wayar. Ido ta kwalalo waje da dafe bakin. Sai kuma ta janye da faɗin, “Kai kamarfa daga cikin wayar ne sautin nan ya fito wlhy. Kai ina”. Ta sake faɗa tana ɗan wawwaigawa babu dai alamar wani a ɗakin sai itan kaɗai. “Oh ni Iffah anya bakin nan nawa bazai yankani ba wataran, yanzu hakama shine yazo ya amshi wayar inata zuba ban sani ba”. Tai tagumi cikin takaicin kanta. Kamar kuma wadda aka ɗan zabura sai ta sake ɗaukar wayar. Cikin sa'a tai tozali da ganinsa online har an amsa mata sallamarta ma. Sai kuma ta shiga kokwanton tayi magana ko kawai ta share. Wata zuciya ta amsa mata da (Kema kin san bashi bane ya ɗaga miki waya. Ki basar kawai). Da alama ta gamsu da shawarar, dan haka ta saki murmushi da buɗe saƙon. “Sorry kin kirani bana kusa yarona ya amsa”. Amsar data samu kenan bayan sallamarta da aka amsa. Har cikin rai taji daɗi, dan haka a fili ta furta “Alhamdullah dama naji haka a jikina”. Shi kuma ta bashi amsa da “Babu damuwa Sir”. “kina da fahimta Shahrbano”. “Bankai nan ba😣”. Ta bashi amsa da emojin yamutse fuska. Sharewa yay da faɗin, “Ta samu ne?”. Itama sai ta share da bashi amsa da. “Kusan haka. Sai dai a wannan gaɓar lamarin akwai ban tsoro Sir Ajmaal. Da gaske mutanen nan matsafa ne kuma suna aiki da aljanu”. “Ya arrahaman! Kamar ya? Har kimsa na tsorata fa”. “Tab tunma kan na faɗa kenan. To kama cire dan wlhy ba aljanu ba ko bataliyar ifiritai ce sai naga bayan mutumin nan. Wai fa jiya da dare nabar sashen nasa na koma inda sukace nawa kawai yau na wayi gari na ganni an sake maidoni sashen Dodon nan. Ɗakin dana kwana kuwa duk da haɗuwarsa na rantse maka a harmutse kamar anci dambe”. “Dambe fa?”. Ya share zancen farko ya amsa na ƙarshe. “Wlhy kuwa Sir! Sai dai fa ni wannan bai damenba. So nake nasan ta yaya aka ɗakkoni aka maido ni inda ba nan na kwanta ba”. “Kina da gaskiya dan akwai alamar tambaya kam. Amma ke yanzu wane mataki kika ɗauka?”. “Komai banyiba har yanzu, nadai fara bincika irin kamshin da naji jikina nayi, inma shine ya aika aljanunsa suka ɗakkoni dan ya kashe ni”. “🤭”. Ya bata amsa da emojin rufe baki alamar tare dariya. “😞Bafa abin dariya bane wannan, abin a dubane. Idan kuma aka halakani kafin ƙwato muku ƴancinku ku kukayi asara Sir Ajmaal”. “Eh gaskiya hakane kuma ranki ya daɗe. Yanzu dai ƙarasa bani labarin dan in san ina zan kama. Saboda na gama shirye-shiryen buɗe wani sashe na shiri na musamman akan wannan case ɗin, sai dai komai zai kasance cikin hikima”. “Aiko da naji daɗi Sir, dan gara kam a fara kafin ma na mutu na dinga ji. Dama inason maka zancen wancan tashin bomb ɗin, ko ka san mutumin nan ko damuwa bai nuna ba akan lamarin tsabar bai ɗauki rai bakin komai ba. Wlhy naji kamar na shaƙesa a jiyan kowama ya huta dan takaici”. “Wai da gaske kike zancen nan ranki ya daɗe?” “Wlhy kuwa babu wasa. Ni ka daina kirana da wannan sunan bana so”. “Kiyi haƙuri kin cancanta ne ai. Zawjata-almilk guda ai ba abin wasan mu bace. Nima dai tsaurin ido yasa har nake iya zaman tattaunawa da ke”. “🙄😏”. Ta tura masa tana kashe data ɗinta. Daga can Ajmaal ya ƙurama emojis ɗin ido yana mai ƙoƙarin danne dariyarsa amma hakan ya gagara, dole yay faffaɗan murmushi har haƙoransa na bayyana yana ayyana (ƙuruciya daɗi) a zuciyarsa. Ganin ta kashe datan shima sai ya kashe kawai dan yana son sai ya nutsu yay zaman nazari akan abinda suka tattauna ɗin..... ★★..... KAUYEN JUMNA ★...... Alhamdullah dawowar Kaka da tsayuwar daka akan lafiyar Ummu yasa jikinta ƙarayin sauƙi har tana ɗan yin magana. Wani lokacin ma idan suna ƴar hira takan ɗan saka bakinta musamman idan akan Iffah ne da a mafi yawan lokuta take faɗo musu a zukata. Bawai halin da suka shiga kansu Babiy ya mantar da su ita bane, a koda yaushe tana manne a rayukansu, suna kuma binta da addu'a da cigaba da baza kunnen saƙon mutuwarta kamar ƴaƴansu na baya. Duk da dai ga Iffahn na nan shafe wata na uku kenan a daular ruman ɗin. Yau ma kamar kullum Ummu da Iyyani na a tsakar gida suna aiki wanda kusan Ummu ce keyinsa duk da bana kirki bane. Kaka ya fita tun ɗazun wajen jana'izar mutuwa da akayi ta wani tsoho. Sauri-sauri Ummu ke ƙarasa aikin saboda rana ta ɗaga gata da zafi sosai kasancewar su yankinsu akwai sahara, danma suna ɗan samun sassauci dalilin ruwa ne zagaye da ƙasar tasu. Sai dai kuma zaman Dahab City (Daular ruman) kamar a tsakkiyar ƙasar ta ruman yasa su sunfi samun zafin yashin fiye da sanyin ruwan daya mamaye wasu jahohin dake a gaɓarsa sosai. Sallamar da akayi ta saka Ummu amsawa tana mai duban ƙofar gidan, Iyyani ta fito tana faɗin, “Inaga mutanen Abbunku ne da basa ƙarewa. Gashi kuma bai dawo ba har yanzu ko yaya zamuyi kenan?”. “Nima shi nake tunani Iyyani, kona leƙa na gani tunda ba'a sani ba ko baƙon mai muhimmanci ne?”. Har Iyyani ta buɗe baki zata bama Ummu amsa sallamar Kaka ta katseta. “To Alhamdullah gamashi nan”. Iyyani ta faɗa tana kallon Ummu. Cikin fara'a kaka ya shigo, hakan yasa bayan sun masa sannu Iyyani ke tambayarsa ko lafiya?. Fuskar tasa da murmushi har sannan ya ce “Bani abun zama kedai yaron nan ne Zakariyya makwafcin su Jumimah”. Ya kare maganar da kallon inda Ummu take. “Ah Masha ALLAH, ALLAH yasa muji alkairi to”. Iyyani ta faɗa tana ɗakko masa abinda ya buƙata har da ruwan sha ma a kofi....... ★★★.... ★★..... ★..... Iffah kam dake ta faman tsuke fuska ita a dole taji haushi ta jawo rigar ɗazun ta maida a saman gown ɗinta ta fice. Isowarta falon dai-dai isar da sakon Tajwar Eshaan akan sake dafa masa shayi a bakin hadimin nan ga masu dafa abinci. Kai tsaye mamaki ya bayyana ƙarara a kan fuskarta. Amma sai ta dake babu alamarsa a zahiri taima hadiman wani kallo ta ɗauke kai. Ba ƙaramin razana da ganinta a cikin kicin masu girkin sukai ba. Dan hakan zai iya zamar musu rasa aikinsu. Sai dai yanda tai kicin-kicin da fuska ya sasu kama kansu, kwarjininta da gizagonta na kere yawan shekarunta. Jikinsu har rawa yake lokacin data buƙaci ganin kayan shayin da Tajwar ɗin ke amfani da su. Daki-daki take binsu da kallo cike da nazari, sai da ta gama tsaf kafin ta juya garesu fuska a tsume. “Idan ina buƙatar wasu bayan waɗan nan a yanzun fa?”. Cikin mamaki da tsoro suka sanar mata za'a kawo da gaggawa. “Ina buƙatar zama da mai kawowar”. Ta faɗa a gadarance da juyawa ta fara haɗa kalar shayi da salon dabararta batare da tayi amfani da wanda ake dafa masan ba. Wannan duk cikin shirinta ne na son ƙuntata ma zuciyar Tajwar Eshaan a cewarta. Cikin lokaci ƙalilan ta gama kasancewar ba wani mai yawa bane, ta juyesa a haɗaɗɗen butar shayi tare da haɗa komai na buƙata tai ƙoƙarin ɗauka. Da sauri hadima ɗaya ta miƙe ta amsheta. Bata musaba wajen bata dan dama ba sanin inda zata samesan tai ba. Hadimar tai tsaye a dai-dai ƙofar ƙaramin falon alamar iyakar ta kenan. Iffah ta fahimci haka, sai kawai ta amsa batare da tace komai ba. Ba tsoro ko shakkar haɗuwa da shi take ba, abinda zai farunne idan ta shiga kawai take tunani. Tsahon minti biyu kafin tai ƙundunbalar shiga dan a ganinta wannan wata dama ce ta biyu a gareta, cikin takunta na nutsuwa da dakewarta ta tura kai bayan ƙofar gilashin ta zuge da kanta batare data tabata ba.........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_42_* .........Kasancewar Barrister Akeem ba baƙo bane na shigowa gidan masu hidima a gidan suka dinga gaidashi. Amsa musu Barrister Abdallah ya dingayi da fara'a da kuma muryar Barrister Akeem data zama yana kwaikwaya a yanzu kamar yanda aka horar da shi. Ya iso katafaren falon da yaji komai na more rayuwar duniya, ga kamshi na tashi irin wanda aka san duk wani jinin ƙasar ruman da shi. Cikin girmamawa ya kai zaune fuskarsa da murmushi ya shiga gaida babban mutum ɗin dake zaune a falon cikin shigar kayan ƙasar na alfarma.      Da ƴar sakin fuska mutumin ya amsa masa da faɗin, “Barrister sai yau ake ganinka? Bayan kuma tun jiya nasa a sanar maka na dawo ƙasar”.          “Amun afuwa ranka ya daɗe, an ɗan samu wani tazgarone daya riƙeni a dalilin zaman da Boss namu ya kira, nayi zaton zamu tashi akan lokaci harna iso nan ɗin sai hakan bata yiwu ba, ganin dare yayi kawai na wuce gidan dan nasan kana bukatar hutu”.     “Hakane kam. Yaya aikin naku?”. “Alhamdullh ranka ya daɗe munata bubbugawa”.          Murmushi mutumin yayi, sai kuma ya ɗan gyara zamansa da zuƙar shisha ɗin hanunsa yana gyaɗa kai. Shiru ya biyo baya kasancewar ɗaya daga cikin masu masa hidima ya kawo ma Barrister shayi. Sai da ya kammala ya fice mutumin ya ajiye marikin shisha ɗin da fesar da uban hayaƙin daya tara a bakinsa.    “Barrister dama ina maka wani neman gaggawa ne akan abokinka mai shegen taurin kai Barrister Abdallah Aas”.        “Tofa oga ya ƙara yin wani laifi ne?”.     “Kusan haka kam, dan akwai wani case na aminina dake a rufe sai ƙoƙarin ganin ya buɗosa yake yi. An masa gargaɗi kusan sau uku amma bai ji ba har sai da yajama kansa aka kauda shi kasan mutumin na ka da taurin kai”.          “Kauda shi kuma ranka ya daɗe?”.    Barrister ya faɗa cikin nuna rudanin as shine Barrister Akeem. Murmushi mutumin yayi irin nasu na manya yana ɗage kafaɗa alamar ko'a jikinsa. “To in basu kaudashi ba mi kake so suyi Barrister?. Yana da taurin kai ne gaskiya. Nasan dai kaji zancen tashin bomb ɗin can na jihar Hubab..?”       “Yes Yes ranka ya daɗe, ai kowa ma dake ƙasar nan yaji wannan baƙon al'amari mai tada hankali tunda bai taɓa faruwa ba a wannan ƙasa tamu......”     “To ga abokinka kam yaja ya faru, dan an tada wannan bomb ɗinne da shi kasancewar a cikin motarsa aka sakashi”.     A matuƙar razane Barrister ya furta “What! Ranka ya daɗe abokin nawa?”.         “Kaga kwantar min da hankalinka wannan ba wani abu bane. Sakamakonsa ya amsa a hannunsa. Kaga ko anan gaba masu shirin taurin kai irin nasa sai su kiyaye. Ba wannan ne abin damuwa bisa maƙasudin kiranka nan ba. Muna son ne ka maye gurbinsa a wancan case ɗin ne domin kwaso mana dukkan wasu bayanai da ya haɗa. Mun zaɓoka ne saboda kamaninku ɗaya, har yanzu kuma babu wanda yasan da shi bomb ɗin ya tashi. Kafin masu bincike su gama gano motarsa ce wadda bomb ɗin ya tashi a ciki muke bukatar ka kamla komai”.        “Amma ranka ya daɗe......” Hannu ya ɗaga masa da sauri. “Karkace komai Barrister, nasan zafin rasashi kakeji, ina maka ta'aziyyar hakan. Sai dai ka sani, wanda ya ɓatar da shi kaima zai iya ɓaddaka kai da duk a halinka wannan yafi shan shayi sauƙi a garesa. Dan haka ka kula. Akwai saƙo na kafin alkalami a motar ka mu yini lafiya🙏”.        Hakan da yay na nufin ya sallamesa. Barrister Abdallah ya miƙe jiki a sanyaye. Gaba ɗaya tunaninsa ya rabu da zuciya da kwakwalwarsa. A yanzu kam ya gagara fahimtar komai gaskiya. Shin idan har waɗan nan ɗin sune mugaye a garesa, waɗan da kuma su yake bibiya a case ɗin su Babiy to sukuma waɗan da suka sakashi wannan aikin fa? Kenan fa kuɓutar da shi sukai a waccan ranar ko mi abinda sukai ɗin ke nufi? Ya ALLAH mike shirin faruwa da ni ni Abdallah?.       Ya tambayi kansa batare da yasan ina zai kama ba har ya ƙaraso jikin motarsa ya shiga. Da ƙyar ya iya tuƙin zuwa waje, yana hawa titi ɗan nesa da gidan aka dakatar da shi akan cewar yay parking ta cikin bluetooth ɗin kunnensa. Hakan ba karamin taimako bane a garesa, dan a yanda yake jinsa tabbas zai iya kife kansa a titin ma gaba ɗaya........               ★★....  ★★.....          Babu kowa a ɗakin sai wani irin ƙamshi mai matuƙar saka jiki kasala da sanyin ac. Iffah ta lumshe manyan idanunta tana ambaton sunan ALLAH da sake buɗesu. (Kai kai kai duniya fa na inda take) ta ayyana a zuciya tana dire tray ɗin hannunta saman wani ɗan table dake gaban ƙyaƙyƙyawar kukera ta hutawa. (Dama ce fa wannan) ta zabura dalilin wancan furucin da zuciyarta ta ayyana. “Tabbas dama ce kam”. Ta maimaita a fili tana ɗan waige-waige a nutse cikin hikima kuma ɗan gudun kar ya zam akwai camara a ɗakin kamar yanda aka bazasu ta waje ko'ina a sashen. Adai iya dubanta babu kamar sauran ɗakunan data kwana, dan haka ta cire takalmanta cikin sanɗa ta nufi ƙofar toilet da zuciyarta ke raya mata yana ciki. Tabbas yana cikin kuwa dan jin motsin ruwa. Ta daga hannayenta sama alamar Alhamdullah sannan ta baro wajen. Da ma'ajiyar turarrukan sa ta fara, sai da ta gama ɗagasu ɗaya bayan ɗaya ta shinshina. Sam babu alamar irin wancan, cikin damuwa ta maida ta rufe badan zuciyarta ta wankesa da zargiba har yanzu. Dan ta gama haƙƙaƙewa aljanun tsafinsa ya tura suka ɗakkota a daren na jiya dan ya cika burinsa. Amma ALLAH ya hanashi sa'a shiyyasama taga ɗakin kaca-kaca kamar anyi dambe a cikinsa. Da alama sun gusar mata da hankaline shiyyasama bataji sanda aka ɗakkotan daga can ɗin ba.      Harta juya zata fita zuciyarta ta sake nata shawarar ta ɗan sake duddubawa ko zataga wani shaida da suke buƙata akansa. Cikin yanayin dai ɗan tsoro-tsoro na mara gaskiyar dake gudun a kamasa take ɗan buɗe-buɗen ta, sai dai abin mamaki idan ka cire turarrukan data gama dubawa, da wasu tarin books a cikin wata ƙyakykywan show glass, babu wani abu a ɗakin bayan kayan gado da na ƙawata adon ɗakin kuma. Sai kuma kayan barci kala-kala a cikin wani dogon gilashi shima alamar matsayin wadrub, sai dai kasancewar zallar gilashi komai ana gani fes dan duk rataye suke a jikin hanger ma.      Iffah da gaba ɗaya kanta ya kulle na mamakin ina kayan da yake sakawa? Da takalma? Su agogo dama duk wani nau'in kayan da yake ado dasu fa?. Dan acan ma sauran ɗakunan da ta kwana iya irin abinda ke anan ɗin kawai ta gani. Lallai dole akwai abinda yake buƙatar tayi nazari a kansa kenan? (Minene to?) Zuciyarta ta ayyana mata tare da katse tunaninta sakamakon jin wani masifaffen kamshin shower gel da tsumammun turarrukan wanka ƴan asali da bata taɓa shaƙar irinsu ba.        A ɗan firgice ta juyo, sai kuma ta sake juyawa da sauri tana mai rumtse idanunta da faɗin, “Wayyo ni Iffah” ta nufi ƙofar fita da matuƙar sassarfa tamkar zata kifa dan hatta da tsumar jikinta a bayyane take..            Shiko da komai ya faru dominsa babu alamar hakan ya damesa. Dan ko kallon inda take baiba tunda ya fito. Babu ma alamar yasan da ita a ɗakin tattare da shi. Amma abin mamaki sai gashi ya zauna a kujerar da table ɗin ke tare da ita, wanda kuma anan ne Iffah ta ajiye shayin nasa. banbancin ɗanɗano da wanda ya saba sha kamar ɗazun ya sakashi yin tsamm da tsurama shiyin ido tamkar a cikinsa yake neman amsar sanin yaya hakan wai ke faruwa?. A zahiri ko babu wani abu a fuskarsa sai ma glowing da take irin na mai lafiyayyar fatar data jiƙu da hutu da jin daɗi. Yatsunsa biyu ya ɗan kai saman goshinsa ya murza kusan tsahon sakanni arba'in, kafin kuma ya janye yana mai ajiye kofin ya miƙe batare da ya sha ba. Ta can wajen gilashin da kayan barcinsa suke ya taka, hannunsa ya daura akan gilashin sai gashi gaba ɗayan drawer ɗin ta zuge a hankali ƙofa ta bayyana. Takawa yay ya shige, ta maida kanta ta zuge........         (😏😏an wani rufe dan kar na gani, to Iffahn mu zata gano mana ai ehe🚶😞).      ★★.....   Da gaske dai ɓatan Sayeed Khairul-Bashar ya tabbata a cikin masarauta. Dan Iya duk wani bincike babu wata alama ta yana a cikin gidan. Iyalansa sai kuka suke duk sun hargitsa masarautar. (Kamar yanda kukaji a baya Sayeed Khairul-Bashar Aami ne a wajen su Tajwar Haysam, Miran Arshaan, Miran Jasim da dai sauransu. Kaka kenan a wajen Tajwar Eshaan shi kuma. Sayeed Khairul-Bashar da Tajwar Abdul-majeed kakan Tajwar Eshaan ƴan uba ne suma. Kamar yanda a yanzu Tajwar Eshaan ke shan gwagwarmaya a hannun su Miran Jasim haka mahaifinsa Tajwar Haysam yasha wannan wahalar a hannun Aamin nasu irin su Sayeed Khairul-Bashar. Sai dai ko kusa basu ci galaba ba dan Tajwar Haysam ma dai kaifi ɗaya ne kuma tsayayyen mutum kamar yanda kuke ganin Tajwar Eshaan a yanzun. Wannan rashin nasarar tasu akan Tajwar Abdul-majeed da ɗansa Tajwar Haysam ce ta dawo kan Tajwar Eshaan a yanzu, sai dai kuma da alama bazai taɓa ya raga musu ba. A gefe kuma su Miran Jasim na amfani da wannan damar wajen dama garinsu akan Tajwar Eshaan... ALLAH ya sa kun gane ni dai ba ruwana🥱🚶)         Duk bidirin da ake Tajwar Eshaan bai sani ba, dan yau ya fita fada ne a makare. Koda ya isa fada kuma aka kawo zancen da farko bai ɗauka abin na gaske bane, dan haka cikin halin ko'in kula irin nasa ya nuna musu maybe yayi fitar da kowa baya buƙatar ya sani ne. A bashi lokaci a gani. A cikin wasu ƴan majalissar tasa wasu sun gamsu da wannan jawabi, harma aka fiddashi waje dan hankulan mutane su kwanta. Sai dai a wani gefen kuma jawabin Shahan-shan ɗin tamkar samun wani makamine na dukansa da shi ga maƙiyansa na ɓoye dana zahiri, sai dai sun danne a yanzu basuce komai ba suna jiran lokaci........      ★★..... BARRISTER ★★.....     Ruɗanin da Barrister yake ciki ya wuce duk yanda mai hasashe zaiyi tunani. Gashi tunda suka maidashi gidan suka sake kullesa a ɗakin babu wanda ya waiwayesa har duhun magriba ya kawo, bayan idar da sallar isha'i ne aka kawo masa abinci. Dan haka ya fuskanci mai kawo abincin da alamar yar yanzu zuciyarsa ta kasa tsayawa waje ɗaya.          “Dan ALLAH ina son magana da ogan ku Akhi. Ina da abubuwan tattaunawa da shi masu yawan gaske da muhimmanci”.     Kamar bazai tanka masa ba sai kuma ya amsa shi da faɗin, “Boss baya nan, ganinsa kuma abune bamai sauƙi ba dan bana jin ma yana ƙasar. Karka damu idan yana buƙatar magana da kai zai zo da kansa basai ka nema hakan ba”. Daga haka yay ficewarsa. Jiki a sanyaye Barrister ya bisa da kallo harya maida ƙofar zai rufe yay saurin faɗin, “Na roƙeka kota wayane ka haɗamu, da gaske maganar da zanyi da shi nada matuƙar muhimmanci, da kuma buƙatar yinta da gaggawa”.      Jimm saurayin yay yana kallon Barrister ɗin daga inda yake, sai kuma ya ɗan rausayar da kansa da faɗin, “Okay duk yanda mukai zan dawo”.      “Nagode sosai”.       Baifi mintuna biyar da fita ba sai gashi, har lokacin Barrister na zaune a inda ya barsa. Ya miƙa masa wayar hannunsa. Cikin jin daɗi Barrister ya amsa. Shi ya fara sallama da gaisuwa batare da la'akari daya girmi boss ɗin nasu ba. Amsa masa akai daga can a taƙaice, nan ma bai nuna ya damu ba cikin tashin hankali ya fara maganar dake cimasa rai..          “Alhmdullah na cika umarninku, sai dai sakamakon dana samo ya matuƙar rikita tunani na. Dan wannan case ɗin case ɗin da nake yine, kuma a dalilinsa naje ƙauyen Lufana. Yanzu kuma sun bani aiki akan kaina, Ina cikin ruɗani sosai, dan na gagara fahimtar manufarku ku da su, shiyyasa gaba ɗaya ruɗani ya kasa barina na fahimci abinda ya dace na fahimta....”      “Karka damu kanka da son sai ka fahimta Barrister. Kai dai kai musu aikin da suka buƙata, basu bayanai akan naka da case ɗin kawai”.     “Idan nai haka zan saka rayuwar bayin ALLAH ne a haɗari, wlhy mutanen na mutanen kirki ne komai an shiryashi garesu ne bisa wata manufa. Ina matuƙar jin tausayinsu, an rabasu da ƴaƴansu har uku, an kuma biyo ta wata hanyar rusasu da shine nake son ma san dalili, yanzu kuma ace nine da hannuna zan miƙasu, idan nai hakan bazan taɓa yafema kaina ba”.     “Baka da wani zaɓi bayan hakan Barrister. Idan kuma ka shirya rasa iyalanka ne fine”. Kitt aka yanke wayar. Barrister dake jin hajijiya na ɗan kwasarsa ya dafe bango da sauri yana mai ambaton sunan ALLAH domin neman ɗauki.........✍️       *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_43_* ..........Yau kwanaki huɗu kenan da rashin ganin Sayyid Khairul-Bashar, kwana shidda kuma cur da kai Iffah sashen Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed. Sosai masarautar a harmutse take, yayinda ƙananun magana da rikice-rikice ke neman tashi a dalilin fitar zantukan da Sayeed Khairul-Bashar ɗin yayi kan Tajwar Eshaan a daren da za'a rasashi. Nan fa kowa ya shiga yima al'amarin fashin baƙi da ga ɓangaren masu faɗa ajin gidan, wanda kai tsaye kusan mafi yawansu sun karkata zarginsu ne da kalaman da Tajwar Eshaan yayi shi kuma..       Duk abinda ke faruwa sarai yana isa kunensa, sai dai abin mamaki yayi biris kamar yanda ya saba. Yayinda shirun nasa ke ƙara wutar al'amarin matuƙa a tsakanin ahalin gidan baki ɗaya. Rashin daɗin maganganun da ke neman kawo bore ga mulkin Shahan-shan ɗin kai tsaye ne ya tada hankalin Malikat Bushirat matuƙa ta nema ganawa da ɗan nata, dan tun ana yi iya su ahali har abu ya zagaye masarauta yana neman fara fita waje.        Bayan mintinan da basu gaza talatin ba amsa daga Tajwar Eshaan ta dawo ga Malikat Bushirat cewar baya buƙatar ganawa da kowa. Ranta ya matuƙar ɓaci da wannan amsa, dan take ta kori dukkan hadimanta ta shiga Safa da marwa. Tasan kota kirashi bazai ɗaga ba, kuma tunda yace bai buƙatar ganawa da kowan ta san halinsa har zuciya baya bukatar hakan. A kaikawon nata Iffah ta faɗo mata a rai, babu ɓata lokaci a karo na biyu ta bukaci ganinta duk da kuwa sune sukai mata katanga da sake baro sashen Tajwar Eshaan tun a waccan fitar acewarsu har sai ta cika kwanakin bakwai ciff.         Iffah na zaune a ƴar barandar da takan sha iska da nazarin littattafan data maida hankali saƙon na Malikat Bushirat ya risketa, ta ɗanji mamaki, amma sai ta shanye a ranta kawai, dan tun washe garin kwananta na biyu Malikat Haseenat ta kirata a waya da kanta ta sanar mata karta sake cewa zata baro sashen Tajwar ɗin har sai kwanakin bakwai sun cika. Haƙuri ta bada bisa kuskurenta, daga ranar kuma ta haƙura duk da a takure take matuƙa da zaman, ganin ranta zaita ɓaci ma a banza sai ta maida hankalinta ga nazarin littattafan nan data ɗibo a books room, ko shi Tajwar Eshaan ɗin ma sai ta ƙulla wasan ɓuya da shi, dan tun faruwar tashin bomb ɗin nan ta riƙesa a rai, sai kuma maganar ɓatan Sayeed Khairul-Bashar da a yanzu aketa dangantashi da shi ya ƙara tabbatar mata da shi mutumin banza ne....        Cikin ƙanƙanin lokaci ta kimtsa, ta saka kamshin data maida nata ta ƙarfi da yaji. Tana fitowa daga sashen ta samu hadimanta na jiranta. Gaisuwarsu ta amsa a yau kam da kulawa, kafin ta shiga motar da zasuje sashen Malikat Bushirat ɗin a ciki duk da bawani uban nisa bane, amma akwai tazara gaskiya. Sojan daya buɗe mata yay salute ɗinta kafin ya maida ƙofar ya rufe, da sauri suma hadiman suka shiga ɗayar motar bayanta.       A tafiyar da bata gaza mintuna biyar zuwa bakwai ba suka iso, anan ɗin ma dai buɗe mata akai, yayinda hadimai ke faman zubewa ƙasa bisa gwiyawunsu. Hannu kawai Iffah ke ɗaga musu da sakewa. Tausayinsu da sake jin zafin wannan mulkin iko na kasarsu a ranta. Tun a falo na farko tabar hadimanta, inda amintacciyar hadimar Malikat Bushirat ta karasa mata iso har inda take.       “Barka da yamma Mah-mah”. Iffah ta faɗa cikin girmamawa ga Malikat Bushirat dake hakimce fuska babu walwala. Hannu kawai ta ɗaga mata, daga haka falon yayi shiru. Sai da ta gama shan kamshinta kafin ta tashi zaune da ƙyau idonta akan Iffah da ta rissinar da kai .     “Ibnati kin san miyasa na kiraki?”. “A'a Mah-mah”. Iffah ta amsata da sauri. Cikin ɗacin murya Malikat Bushirat ta cigaba da faɗin, “Akan mijinki ne, nasan duk abinda ke faruwa a Masarautar nan kin sani kema”.           “Hakane Mah-mah, amma sai nake ganin kamar ba haka bane, kawai dai wasu ne ke son ɓata masa suna”.        Har cikin rai kamalan Iffah sun saka Malikat Bushirat jin sanyi a rai, sai zuciyarta na rawa dan zuwa yanzu al'amarin ɗan nata da gaske tsoro yake bata. Yayinda ita ko Iffah ta faɗi hakanne da manufar wayon da ALLAH ya bata domin son fahimtar abinda take son sani.         Malikat Bushirat ta katse mata tunani da faɗin, “Hakan zai iya zama gaskiya, sai dai bazamu saki jiki ba dan da gaske al'amarin mijinki na bani tsoro. A yanzu haka na bukaci ganinsa amma shi yace bai buƙatar ganin kowa”.      Da mamaki Iffah ta ɗan ɗago ta dubeta, a ranta kam jinjina rashin mutuncin sa take, a tunaninta ai ko kowa bai tsiraba mahaifiyarsa ta tsira.  “Mah-mah kuma shi ɗinne ya faɗa?”.     A karan farko Malikat Bushirat tai murmushin takaici. “Kar kiji ko tantama akan hakan Ibnati. Dan duk yanda kike tunaninsa ya wuce nan ɗin. A yanzu dai tunda ya nuna bai buƙatar ganin kowan bazai gani ɗin ba. Shiyyasa na kiraki nan dan kimin wani taimako na haɗani da shi ta waya”.          Yawu Iffah ta haɗiye muƙut, dan itama dai a karan kanta kwanaki huɗu kenan bata sanyashi a ido ba. Tayaya kuma zata haɗasu a waya. To wanda ma ya nuna kai tsaye bazai haɗu da ita matsayin mahaifiyarsa ba ita kuma ƴar karere taya zatai hakan?. Amma bara ta amsa mata kawai, dan koba komai itama tana buƙatar jin gaskiyar lamarin ai.......         ★★.......    Har lokacin kwanciya barci Iffah bata samu wata makamar riƙewa na tunkarar Tajwar Eshaan ba. Hasalima bata da tabbacin a inda zata samesa. Tambayar hadimai kuma tamkar gazawace a gareta matsayinta na Zawjata-almilk. Kusan ƙarfe ɗayan dare tana tsaka da kai kawonta da faman jan tsaki saƙo ya shigo wayarta. Kamar zata share sai kuma ta ɗauka dan koba komai kullum a cikin tsumayen ji daga su Babiy take. Mamaki ya sata buɗe saƙon da hanzari ganin Malikat Bushirat.       _Ina alfahari da kasancewar ki tare da gudan jinina Ibnati. ALLAH yay miki albarka, yanda kika zama sanadin yaye damuwata kema ALLAH ya yaye miki taki yanzu na gama waya da shi_.      “What!!”. Iffah ta faɗa cikin ɗan zabura tana sakin wayar akan carpet. To mi hakan ke nufi? Ita da batama gansa ba taya har yay kiran mahaifiyar tasa da har ta gamsu itace sanadi. “Anya mutumin nan kuwa ba ifiritin aljani bane?”. Ta faɗa a zahiri tana waige-waige a ɗakin da tunanin ko dai akwai camara, to inma camara ɗin ce itada sukai magana a sashen Malikat Bushirat ma ta ina camara ɗin zatai tasiri kenan...        Har waye war gari babu nutsuwata tattare da Iffah akan wannan al'amarin, dan ko barcin kirki batayi ba sam. Sai dai tuna a'a yau zata bar sashen ya saka mata ɗan jin sassauci ka ɗan a zuciyarta. Tana ko idar da sallar asubahi ta taattara kayanta waje guda tsaf tana jiran gari ya ƙara haske ta kama gabanta duk da kuwa wata zuciyar na bata shawarar take akan zuwa Tajwar Eshaan wai ko zata fahimci wata gaskiya saɓanin wadda zuciyarta ke tabbatar mata. Amma dai ta dake dan tana buƙatar damar keɓance kanta ko zata samu nutsuwa.         A bisa al'adar masarautar kamar yanda ake kai Zawjata-almilk turakar Shahan-shan haka ake zuwa a ɗakkota cikin tattali da giramamawa tare da manyan ƙyaututtuka a randa ta cika kwanaki bakwai cif. Kowa ya ɗauka tunda an kai Iffah ba bisa ƙa'ida ba baza'ai wannan al'ada ba gareta musamman yanda tama karya doka a kwana ɗaya ta fito. Ga kuma a yanda masarautar take harmutse kwana biyun nan. Amma sai Malikat Haseena ta bama kowa mamaki ta hanyar haɗa komai na al'ada da akeyi, tare da mukulllin zabgegiyar mota ƙirar zamani da masu hidima har guda goma, da tarin turarurruka na musamman, Daneen Ammarah da tsaffin dake da hurumin gudanar da al'adar a masarautar suka yima sashen Tajwar Eshaan tsinke cikin busar sarewa mai tabbatar da isar da saƙon manufar al'amarin.       Tofa wannan fa shine an tsokalo tsuliyar dodo. Dan kuma masu rajin faɗa aji tuni sun sake buɗe shafin caccakar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed da kakar tasa Malikat Haseena kan basu damu da ɓatan Sayeed Khairul-Bashar ba. Ko kuma ma dai sun san komai ɗin da gaske. Wannan al'ada ta sake saka jikin Iffah mutuwa da shiga ɗunbin mamaki na gaske, har aka maidata sashinta babu alamar tana cikin cikakken tunaninta ma. Bin dai kowa take da ido tamkar gunkiyar da aka ƙirƙira domin tarihi...      ★Ashe duk wan can ƙarami ne a abin mamaki da Malikat Haseena ta tanada a yau ɗin. Dan ƙarfe tara na dare da kanta kamar yanda tayi akan Iffah ta sake jagorantar rakiyar ɗaya cikin biyun Zawjata-almilk dake gidan tun kafin zuwan Iffah. Duk da bata haɗu da Tajwar Eshaan ba yau bata dawo da ita ba kuma dan acewarta zai ma gaji ne itama ya kulata idan ya gama zaman kulle kansa a ɗakin kamar yanda zukatansu ke basu sakamakon sanin hakan al'adarsa ce a duk sanda ransa ke ɓace.        A wannan gaɓar kam kowa ya saki jiki waccan matsalar ta shuɗe tunda ga Iffah tai kwanakinta lafiya ta fito. Maimakon shiga fargabar rasata itama sai kowa ya ɓige da ƙananun magana akan rashin dacewar hakan. Yau ɗin ma dai malikat Haseenat tayi kunnen uwar shegu da su, yayinda Malikat Bushirat da Daneen Ammarah suka shiga halin mamaki da hukuncin na Malikat Haseenat a karo na biyu saɓanin dukkan shirye-shiryen su. A wannan karon kam sun yanke ƙuirin tun kararta suji ba'asi, sai dai sun barma safiya komai....        ★★      Surutai akan ɗimuwar da aka wayi gari da shi a masarautar ne ya farkar da Iffah dake fashin salla ɗan barcin daya figeta, dama da ƙyar ta yisa sakamakon kwana da tai neman Sir Fawzan da Sir Ajmaal a waya amma bata samesu a online ba hakama a kira. Sai abinda ta karanta da yay matuƙar tada hankalinta a ɗaya daga cikin littafan da take nazarta akan Tajwar Eshaan. “Tabbas babu lafiya” ta faɗa a zahiri tana miƙewa zumbur. Har ta nufi ƙofa ta dawo da sauri, toilet ta shiga a gurguje ta watsa ruwa ta fito. Sama-sama ta kimtsa jikinta ta fito. Hadiman ta da alamun sanyin jiki ya bayyana a agaresu suka dinga zubewa gaisheta. Maimakon amsa ta jefa musu tambayar da ruɗani ya bayyana kansa a cikin idanunsu da jikkunansu lokaci ɗaya.       “Mike faruwa a masarautar nan? Da alama babu lafiya?”.     Duk sun rikice babu alamar wani zai amsa mata. Sai kaɗuwa suke kamar masu jin sanyi. Halin da take ciki ya assasa mata jin zafin hakan ta daka musu tsawa. Sake firgicewa sukai, sai dai wajibi ne a gare su bin umarninta, dan haka cikin ƙarfin hali wadda ke matsayin amintatta a gareta ta sanar mata cewar an wayi gari da rashin Zawjata-almilk ne ta farko da jiya ta kwana turakar Shahan-shan sai Sayeed Khairul-Bashar shima da aka samu gawarsa a wani ɗaki cikin masarautar. Iffah da bata san da hakan ba ta ƙame ƙam alamar sumar tsaye ta wucin gadi ce ta risketa. Sai kuma hajijiya ta fara juya mata falon da hadiman, a hankali duhu ya dinga lulluɓe idanunta data kafa musu tabbacin bata cikin hayyacinta..........✍️       *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_44_*     ..........A hankali ta shiga ƙoƙarin buɗe idanunta da takejin sun mata matukar nauyi, sai kuma ta yunƙura ta tashi da ƙyar tana mai bin ɗakin da kallo. Dishi-dishi take ganin amintacciyar hadimar tata dake rukuɓe gefe ta zabga tagumi, _(An wayi gari da rashin Zawjata-almilk ne ta farko da jiya ta kwana turakar Shahan-shan sai Sayeed Khairul-Bashar shima da aka samu gawarsa a wani ɗaki cikin masarautar.)_ kalaman hadimar na ɗazun suka shiga dawo mata tiryan-tiryan a zuciya. Da karfi ta rumtse idanun nata da sukai jajur, ga kanta dake matuƙar sara mata kamar zai rabe biyu. Amma haka ta yunƙura ta sauka a gadon cikin ƙarfin hali da jarumta, dan idan batai amfani da wannan lokacin ba tabbas damarta ta kuɓuce mata kenan, batajin kuma zata sake samun wata cikin sauƙi. Zumbur hadimar ta miƙe itama tana mata sannu, bata iya amsa ta ba, sai nuni da tai mata ta je. Jiki a sanyaye ta fice, ita kuma ta jawo mayafi ya naɗama jikinta.        Hadimanta dake falon farko duk suka miƙe, hannu ta ɗaga musu alamar bata buƙatar rakkiyar ta fice ita kaɗai dan babu yanda zasuyi. Da gaske masarautar a hargitse take matuƙa, duk da ba wannan ne karo na farko da aka rasa Zawjata-almilk ba, sai dai haɗi da mutuwar Sayyid Khairul-Bashar ta sake girmama ta Zawjata-almilk ɗin itama a wannan karon, da kuma tsallakewar Iffah da aka fara kaiwa babu abinda ya sameta. Cikin dabara da amfani da harmutsewar gidan tai amfani wajen kutsa kai sashen Shahan-shan. Zuwa yanzu fuskarta ba ɓoyayyar fuska bace ga masu tsaron sashen, dan haka babu wanda ya dakatar da ita sai ma gaisuwar girmamawa da suke miƙa mata duk da ganin nata ya basu mamaki. Su kansu hadimai masu girka abincin Tajwar Eshaan ɗin data samu a falo na uku saɓanin na karshe da ta san suna zama ganinta ya girgizasu, musamman daya kasance har yanzu ba'a fita da gawar Zawjata-almilk ɗin ba. Hasalima babu wanda yaga Shahan-shan har yanzu balle jin motsinsa. Kamar yanda tun a ƙasa bata tanka gaisuwar kowa ba anan ɗin ma bata kulasu ba dan ganinsu ya tabbatar mata anan abun ya faru kenan, ita wannan Zawjata-almilk ɗin a ɗakunan barcin falo na uku aka ajiyeta. Duk da bata san ya suke ba babu ko ɗar tattare da ita ta shige abinta inda take kyautata zaton ɗakunan barcin nan ɗin suke.      Ido rufe take bin ɗakunan ɗaya bayan ɗaya, sai dai har kusan uku duk a rufe suke, bata gajiya ba ta cigaba sai a na biyar ta samu a buɗe. Cikin rawar jiki ta afka ɗakin, yayi kaca-kaca tamkar anyi dambe a cikinsa, dan wasu abubuwan ma duk gasu anan a fashe ƙasa, sai ɗigo-ɗigon jini ta wasu wajajen da dama. Idanunta suka sauka akan ƙyaƙyƙyawar budurwar da a shekaru zata iya zama sa'ar Arfa shimfiɗe a ƙasa ta jikin gado. Yanda gashinta da jikinta ke a birkice zai tabbatar maka da ta jigata matuƙa kafin ta rasa ranta, dan hanunta na dama dake kaca-kaca da jini riƙe yake da wata kwalbar filawar doco... Alamar ta riƙe domin kare kanta, amma duk da haka sai da akaci galaba a kanta. Iffah da jikinta ke karkarwa ta durƙushe hawaye na rige-rigen sakko mata, dan ji take kamar Fariha da Arfa ne take kallo kwance. Ta jima tana kuka akan gawar kafin ta zabura sakamakon maganganu da takejin suna tunkaro ɗakin, zumbur ta muƙe ta fara daukar video recording ɗin ɗakin har gawar, sai kuma ta ɗauka hoton gawar ta kowacce kusurwa. Jin shigowar za'ai da gaske tai saurin fara neman wajen ɓuya....          Miran Jasim, tare da Miran Arshaan, shugaban jami'an tsaron masarauta, Daneen Ammarah sai Malikat Bushirat da a wannan karon ta kasa haƙuri itama suka shigo. Sai da suka gama bin ɗakin kaf da kallo kafin su ƙarasa kan gawar. Shiru babu wanda ya iya magana a cikinsu har tsahon wasu mintuna kafin shugaban jami'an ya nisa.      “Exactly kisan irin na baya ne dai babu wani banbanci gaskiya, da alama kuma tayi ƙoƙarin kare kanta itama shine dalilin kasancewar ɗakin a haka harma da wannan jinin”.       “Wannan lamari daban mamaki yake, taya za'ai kisa amma babu wani alamar yanda akayisan, a wannan karon kodai za'a canja likita ne? Dan dole dole akwai abinda yake a ɓoye. Yarinyar nan itace ta goma sha biyar da aka rasa, kisan kuma iri ɗaya babu wani bambanci sai kace abun tsafi”.       “Haba haba wane irin kuma tsafi? Jasim Akh. Dole dai akwai abinda bamu sani ba ɗin kam gaskiya”.      “Zancena nakan hanya Ukhti Ammarah. Idan ba aikin tsafi ba mi zamu kira wannan al'amarin ne? Bagashi ita waccan da yake ta gagara ko kuma wani abu daban ta tsira babu abinda ya sameta ko ciwon kai ba”.         “Inaga yanzu duk ba lokacin yin wannan maganar bane, ayi abinda ya dace, a wannan karon kuma ya kamata Abni yace wani abu bawai ya cigaba da yin shiru ba kamar yanda ya saba”.     “Maganarka nakan hanya Miran Arshaan”. Miran Jasim ya faɗa cikin son sake tabbatar wa. Shiru Daneen Ammarah da Malikat Bushirat basu tanka ba, hakama jami'in yanata cigaba da zagaye ɗakin alamar nazari.. duk wannan al'amari Iffah na maƙure a maɓoyarta tana sauraren komai hannunta danne kan bakinta kar kukan da take ya fito har su farga da ita. Koda suka gama abinda suke bayan shigowar doctor da fitar da gawar kasa fitowa tai, sai dai ta zame ƙasa da sake fashewa da wani irin kuka mai ban tausayin dan mutuwar yayunta biyu ta dawo mata ne a rai sabu a yau ganin ta hanyar da suma suka rasasu a zahiri gabanta......        “Kuka bashi zai kuɓutar dake ba kema...”     A razane Iffah ta buɗe idanunta dake kaca-kaca da hawaye gasu jajur. Miran Jasim da tun ɗazun ya lura da ƙafar Iffah amma ya basar har sai da suka fice yayo sau da baya ne a gabanta. Duk da so ɗaya ta taɓa ganinsa ranar liyafar cin abinci da aka kawota nan hakan baisa ta shaida fuskarba a ɗan fisge.      Kai ya jinjina mata cikin ɗage kafaɗu “Yanda ya kashe na baya kema babu tantama hakance zata kasance. Karki ga ya ƙyaleki zata iya yuwuwa shirinki na musamman ne. Amma in har kin shirya kuɓuta daga tarkon sa ni mai iya taimaka miki ne”.    Iffah dai kallonsa take kamar gunkiya, sai hawayen da suka kasa tsaya mata ne kawai ke tabbatar da ita a mai numfashi. Bai nuna ya damu da yanayin nata ba ya cigaba da faɗin.         “Ni sunana Jasim Ibn Abdull-Majeed Aliy. Ƙani ga mahaifin mijikin kenan. Nasan kina buƙatar sanin abubuwa masu yawa akansa amma kinƙi samun kowacce irin dama saboda iyayensa dake zagaye da ke. Duk yanda kike zaton abin ko tsammani ya wuce nan, Malikat Haseena da Malikat Bushirat da kike gani sun san komai game da mutuwar matansa, hasalima da taimakonsu komai ke gudana, zaki iya lura da hakan a yanzu ta yanda duk muka nuna damuwa amma su ko'a jikinsu. Abinda zai tabbatar miki da sun sani kuwa duba da abinda kika ganema idonki ne, taya za'a kashe mutum amma a kasa gane hakan, sannan kuma a sake kawo masa gobe ta mutu hakan baisa an dakata ba. Waɗan nan likitoci da jami'an da kike gani duk an siyesu ne, shiyyasa suke pretending cewar basu san komai ba ko basu gane komai ba. Koda yake su a zahiri bazasuga komai ɗin ba, dan ana kashesu ne ta hanyar tsafi domin ƙarama ƙarfin mulkinsa iko.....” yaja numfashi tare da fesarwa idonsa a kanta yana nazartar yanayin tasirin da maganarsa ke samu a wajenta. Da alama akwai nasara dan haka ya cigaba da faɗin, “Mu ajiye wannan, dan bashi da amfanin cigaba da faɗa miki. Ko kin san mahaifinki da ɗan uwanki ma anyi amfani da jininsu a maimakon naki shiyyasa ke kika tsira saɓanin wannan”.      Zabura Iffah tai jikinta na rawa. Sai dai ta kasa faɗin abinda ke son fita a bakinta. Ya ɗaga mata hannu da faɗin, “Kinga kwantar da hankalinki, amshi wannan ki kalla. Idan kin kammala sai ki yankema zancena hukunci. Amma ki sani tabbas ta hanyar da aka halaka iyayen nan naki da ita ake bi wajen halaka waɗan nan matan nasa shiyyasa likitoci basa gane komai na barki lafiya..”       Harya ɓacema ganinta Iffah bata iya ta motsa ba, sai dai rawar jikinta da karkarwa a bayyane take. Jin kamar motsin mutane ya sata ɗaukar flash ɗin daya ajiye mata ta sake ɓoye wa. Jami'in ɗazunne ya dawo ɗakin, a wannan karon sun ɗauka hotunan komai a ɗakin da ɗan sake bibbincikawa dan tare yake da yara biyu jami'ai suma. Dole Iffah ta sake lafewa har suka fice sannan itama ta fito.       ★ A yanzu kam masarautar a harmutse take fiye da ɗazun, hakan ya sake bama Iffah damar komawa sashenta cikin matuƙar tashin hankalin abinda ya faru da zantukan wannan mutumi. Kulle kanta tai a ɗaku ido rufe ta saka flash ɗin a jikin laptop ɗinta da bawani amfani dake da shi ba. Abin tamkar wani film video ya fara da shigar Babiy riƙe da Abu Moosa cikin gidansu a waccan ranar, shimfiɗa tabarmar Ummu da bayanin Abu Moosa da bai kammala ba har mutuwarsa. Zuwan matar Abu Moosa da jami'an tsaro abinda Hanash yay mata da tafiya dasu. Daga nan ya yanke. Da sauri tai playing na gaba. A yanzu kam su Babiy ne a mawuyacin hali duk sun rame sunyi baƙi a cikin wani ɗaki. Kan Babiy a saman cinyar Hanash alamar babu lafiya tare da shi, Hanash nata faman shafa masa ruwa a fuska yana kuka. Sautin dariya ne ya fara tashi a ɗakin, kafin shigowar wani mutum da iya jikinsa kawai ake gani babu fuska. A take su Hanash suka zabura yayinda sautin dariya ke tashi da tafa hannayen mutumin. Bayan anyi dariyar mai tsawo aka tsagaita, ƙirjinta yay wata irin bugawa jin muryar Shahan-shan. “A tunaninku bayan samun tagomashi a jinin yaronku ƴan baiwa zan haƙura ne. Ina bazai yuwuba, dan a kaf yaran dana halaka jinin ƴaƴankune na farko daya bani fiye da nasarar da nake buƙata, shiyyasa na fara bibiyar ta uku daku kanku saboda bincikena ya nuna min daga jinin ubansu ne”. Hhhhhhh! Hhhhh!! Kune nasarata ahalin Zayyan. Kune nasarata dole ne kuma na samu hhhhhhh!!!”.      Kuka Hanash keyi da roƙonsa amma babu alamar zai sauraresa. Sai ma wani irin salon siddabaru da yakeyi da hanunsa a take ɗakin ya turniƙe da hayaƙi, sai kuma wata irin guguwa mai ƙarfi ta nannaɗe hayaƙin a tsakkiyar ɗakin. Su Babiy dai tuni sun maƙure a bango. Sai kuma suka shiga ihu ganin guguwar ta zama wani irin maciji daya kusa cinye kashi ɗaya bisa ukun ɗakin, sara ya fara kaima su Babiy da suka dunƙule waje ɗaya shi da Hanash, kafin macijin ya kafa kansa a wuyar Hanash dake ƙanƙama Babiy. Tuni duhu ya gama mamaye jikin Iffah dake karkarwa, ta rufe laptop dan zuwa yanzu ma kukan ya kafe ƙaf a idanunta. Sai wani irin mahaukacin ja da sukayi kai kace wuta aka haɗa a cikinsu. Tun tana iya jin surutan masarautar har ta daina jin komai. Daga haka sai farkawa tai ta ganta a gadon asibiti Daneen Ammarah tare da ita..      Gaba ɗaya ta tsani komai daya shafi Tajwar Eshaan. Dan haka tun buɗe idon farko da tai ta ga wadda ke tare da ita bata sake yarda ta buɗe ba.  Hakan yasa Daneen Ammarah bata san ta farka ba. Dama itama kuma tayi matuƙar nisa ne a cikin tunani a kallo ɗaya ma zaka fahimci bata tare da nutsuwarta. Ga wata ƴar rama ta yini ɗaya sakamakon tashin hankalin da ake ciki tattare da ita. Dan tun kai gawar Zawjata-almilk da Sayeed Khairul-Bashar makwanci ba daular ruman kawai ba gaba ɗaya ƙasar ruman a harmutse take. Yau wasu a cikin talakawa sunyi ƙarfin halin fitowa zanga-zanga a wasu jahohin suna kiranyen Shahan-shan ya sauka ko su ɗauka doka a hanunsu.      Fitsari daya takura Iffah ne ya tilastata tashi har Daneen Ammarah ta farga. Da sauri takai hannu ta riƙota tana mata sannu, dauriya kawai Iffah tai na dannewa dan tunanin datai a ɗan farkawar nan Tata zuciyarta ta bata shawarar ɓoye sirrin ranta domin samun cikar burinta. Dan tayi alkawarin a wannan karon sai ta halaka Shahan-shan, ta riga ta ƙuna bata tsoron mutuwa. In har burinta ya cika danta mutu ba komai bane a gareta a yanzu ma tafi buƙatar mutuwar fiye da rayuwa tunda har ta rasa sauran ahalinta kuma miya rage mata.         “Ya akai na zo nan Mamy?”. Ta faɗa cikin danne komai dake ɓoye a ranta. Daneen Ammarah da farin cikin farkawar Iffah ya sata sakin murmushi yaƙe da ita kuma Iffah ta fassara da wani abu daban ta amsa mata da faɗin, “Sakamakon abinda muke tunanin ya rikeki aka sameki a sume shine aka kawoki asibiti, amma Alhamdullah tunda gaki kin farka”.     Maimakon ta amsa mata wannan zancen sai ta jefa mata tambaya. “Mamy da gaske ta mutu ko?”.         Take idanun Daneen Ammarah suka cika da hawaye. Cikin ɗaci tace, “Sun kasheta Ibnati, sun sami damar da suke buƙata akansa. Gaba ɗaya ƙasa ta harmutse da bore akansa kamar yanda dama suke son cimma buri”.      Iffah ta ɗan lumshe ido ta buɗe zuciyarta na karajin tsanar Daneen Ammarah ɗin da mamakin salon yaudararsu, amma a zahiri sai itama ta marairaice fuska. “Mamy ban fahimta ba?”.      Hawaye Daneen Ammarah ta share, “Ibnati a yau ruman baki ɗaya a harmutse take, talakawa nata zanga-zanga a wasu jahohin akan sai Abni yayi murabus a kujerar Shahan-shan inba hakaba zasu ɗauki mataki. Gashi tunda abin nan ya faru babu wanda yaga idonsa ya kulle kansa a ɗaki anyi-anyi ya buɗe yaƙi”.        Iffah ta rumtse idanu da karfi tana taune lips ɗinta, yayinda take faɗi a zuciyarta da kakkausar murya. (Ni zan ƙarasa musu aikin da kawo musu ƙarshen matsalarsu. Dan ba murabus kawai ya cancanci yi ba mutuwa gaba ɗaya yabar duniyar ya cancanta da shi ba kujerar Shahan-shan da ƙasar ruman kawai ba)..........✍️  *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_45_*      ........Daneen Ammarah dake tunanin yanayin ma Iffah tashin hankaline kawai sai ta shiga rarrashinta. Dole Iffah ta cigaba da pretending da matsawa a sallameta taji sauƙi. Daneen Ammarah na rakata sashen ta wuce dan jikin Malikat Haseena ma dai babu daɗi sam. Dama Daneen Ammarah ɗin ta zauna da Iffah ne domin saka ido kar wani ya cuta mata itama. Hakan yama Iffah daɗi, dan ya bata damar nutsuwa a kallon videon data ɗauka ɗazun. Sosai tai zooming gawar Zawjata-almilk tana kai bin jikinta ta inda yake a waje daki-daki. Wata irin zabura tai ganin abinda take ma ɗin kuwa a saitin wuyan gawar ta gefen kunenta na haggu. Wato alamar ɗigon sarin maciji har biyu. Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un take ambata wata irin zufan na keto mata, dan kuwa tabbas zancen mutumin can ya zama gaskiya. Amma duk da haka tana buƙatar sake tabbatar wa. Cikin rawar da jikinta ke mata ta shiga laluben number ɗin Sir Fawzan. Bugu ɗaya kuwa ya amsa kasancewar dama a jirace yake da kiran, dan ya nemeta amma bai samu ba. Yaci kuka har ya godema ALLAH dan zatonsa ma ita suka rasa. Cikin rawar murya ya ambaci sunanta duk da yaji muryarta. Amsawa tai da kuka, bata jira cewarsa ba tace, “Sir kaji tsoron ALLAH ka sanarmin gaskiya akan iyayena. Na rokeka karka ɓoyemun komai”. Zufa ce ta shiga karyo masa tako ina, dan baiyi tunanin jin wannan tambayar bazatanba a bakinta.      Shirunsa ya sake tada hankalin Iffah, ta cigaba da masa magiyar da dole ya faɗa mata gaskiyar data buƙata. “Tabbas na ɓoye miki Iffah, amma tun bayan barinki gida baifi da kwanaki ba aka rasa ɗan uwanki da Babiy sakamakon......”     Ya zayyane mata labari tiryan-tiryan kamar yanda ya bincika. Babu kuma banbanci da abinda ta gani a wancan video ɗin na farko. Ya kare da faɗin, “Wlhy har yanzu akan binciken inda aka kaisu ake amma babu labarinsu. Nima kuma a yanzu haka ina yin nawa ta ƙarƙashin ƙasa amma har yanzu ban samu wani bakin zaren ba....”      Kukan data fashe masa da shi ne ya katsesa daga jawabin nasa. “Ba zaku gansu ba, ba zamu ƙara ganinsu ba, sun rabani da su kamar yanda suka rabamu da ƴan uwana. Wlhy nima sai na kasheshi kamar yanda ya kashesu. Na rantse bazan barsa ba, bazan taɓa barinsa ba. Yanda ya halakasu da macijin tsafi sai na halakashi da dafin maciji na gaskiya. Shima sai ya ɗanɗa......” kuka ya sarƙeta ta kasa cigaba da magana...       Cikin tashin hankali daga can Sir Fawzan ke faɗin, “Iffah ban gane ba. Dan ALLAH ki daina kuka kimun bayani, kaina ya kulle dan ALLAH kiyi shiru kinji, wlhy na miki alkawarin taimaka miki akan koma minene, koda kuwa nima zan rasa rayuwata ne.....”.     “Babu wannan lokacin sir, bani da shi. Kai dai kawai ina zan samu dafin maciji mai haɗarin gaske?”.    “Ya ALLAHU! dan ALLAH ki faɗamin mike faruwa? a yanda zan fahimceki”.        “Idan bazaka samamin abinda nake buƙata ba na Barka lafiya”.     Yana hello-hello bata sauraresa ba ta yanke wayar, koda ya sake kira bata ɗauka ba, da taga zai dameta ma sai ta jefa shi a black list. Kaikawo ta cigaba dayi a ɗakin tana kuka. Komai ya cakuɗe mata, zuciyarta ta gama ƙeƙashewa da bushewa. Ta sallama duk wani ɗan sauran rangwamenta. Abinda kawai idonta da zuciyarta ke gani gawa huɗu ta ahalinta kwance duk a dalilin mutum ɗaya tak, lokaci yayi da zatai abinda ya kawota itama dan bai cancanci cigaba da rayuwa ba mutumin nan sam, tayi alkawarin tare zasu mutu, amma sai ta kasheshi ta kuma bayyanama duniya wanene shi.       Yanda taci kuka ta fita hayyacinta dole ta bama duk wani tausayi, da ƙyar ta iya zaman rubuta komai da ya rage, ta tattare ga Ajmaal, a ganinta ta gama tattare dukan abinda ya dace ta tattare masa. Hatta ƙudirinta na kawar da Shahan-shan ta hanyar dafin maciji bata ɓoye masa ba. Ta kwashe videos ɗin dake wayar zuwa wayarta ta turama Ajmaal ɗin, takumayi gajeren video da kalaman masu girgiza zuciya har biyu. Ɗaya na Ummu da su Kaka ta roƙa ya bamawa, ɗaya kuma na al'ummar ƙasar ruman ne baki ɗaya. Shima tai masa godiya da fatan alheri da nasara har ƙarshen rayuwa.......           ★★..... BARRISTER ★★.....       Barrister dake jin kamar ya ƙwaɗa wayar da ƙasa ya rumtseta a hannunsa da masifar ƙarfi, a karo na farko wasu zafafan hawaye suke silalo masa. Jarumar zuciyarsa zugasa take kada ya yarda ya amince koda zai rasa rayuwarsa, yayinda wani ɓangaren kuma ke haska masa iyalansa da yafi so fiye da komai a duniya a halin yanzun. Wannan shine tashin hankalin mafi ƙololuwar girma daya taɓa cin karo da shi a rayuwarsa....         Washe gari da safe wujiga-wujiga ya wayi gari, amma hakan bai saka ko gezau ga mutanen ba. Sai ma duk wani details daya shafi case ɗin da suka dire masa. Mamaki da tsoronsu ya sake mamayesa ganin duk wani abinda ke hannunsa ne. Kuma ya adanasu ne a mabanbanta wajeje. Akwai wanda a gidansa suke, akwai wanda a office suke, akwai na mota ma. Amma abin mamaki gasu duk a gabansa sun tattaro sun kawo masa. Tabbas ya sadaƙar, dan mutanen nan hatsabibaine na innanaha. In har zasu iya hakan a kankanin lokaci bayaji idan ya bijire musu iyalansa zasu tsira kuwa....       “Barrister baka da lokacin dogon tunani, ka shirya dan a yau oga ke son ka tattaro masa duk bayanin da yake buƙata a wajen mutanen can. Ciki har da sanin su wanene ainahin masu aikin, da inda suka ɓoye Abu Hanash da ɗansa”.     Karan farko Barrister ya dubeshi a razane, har ƙoƙarin taune harshe yake wajen faɗin, “Kana nufin dama baku bane ke riƙe da su Abu Hanash ɗin...?”           Saurayin yay ɗan waige-waige alamar baya son wani yaji, cikin raɗa-raɗa yace, “Bamu bane Barrister. Muma kuɓutar da su muke son yi har ma da kai kanka. Sai dai ban san miyasa oga bai son ka sani ba ya zaɓi baka aikin a kife”.     Ba ƙaramin zabura Barrister yay ba jikinsa har rawa yake ya matsa gab da saurayin. “Dan ALLAH kada ka yaudareni ka faɗa min gaskiya”.     Da sauri saurayin ke masa nuni da yay ƙasa da murya kar wani yaji, “Barrister wlhy kaji na rantse maka abinda na faɗa maka shine gaskiya. Na kuma sanar maka ne saboda ka bani tausayi. Amma iyalanka kansu suna zagaye da tsaro ta yanda wani bazai taɓa iya samun damar cutar da su ba, kai kanka kusan sati uku fa muna tare da kai batare daka sani ba. Oga ba azzalumi bane ba, amma ban san miyasa bai son kasan taimakonku zaiyi ba. ya kamata kaima ai ka gane hakan tun farko musamman aikin daya baka ɗin, taya wanda zai cutar da kai zai kuɓutar da kai?, taya wanda zai cutar da kai zai ɗauraka akan hanyar abinda kake nema ya baka bakin zarensa haka cikin sauƙi?”.      “Hakane wlhy ɗan uwa hakane. Kaina ne ya kulle a ruɗani nake gaba ɗaya. Nagode nagode yanzu kam ka bani ƙwarin gwiwa, insha ALLAHU kuma sai na bada mamaki. Dan a wannan gaɓar sai su Abu Hanash sun fita da izinin UBANGIJI, zan kuma gano koma wanene da hannu a kan ɓoyesu”.        “ALLAH ya baka nasara. Ni bara naje kar wani ya fahimci ina anan har yanzu”.    Kai kawai Barrister ya ɗaga masa yana murmushi. Wannan tattaunawa ce ta bama Barrister duk wani ƙarfi da sabuwar himma na musamman, a yanzu kama baka iya ganin komai sai murmushi tare da shi, lokacin da aka kawo masa abincin rana ya buƙaci takarda da abin rubutu. Takardu aka kawo masa bama takarda ba, hakan ko ya masa daɗi, dan ya kwashe sauran wannan yinin da dare wajen tsara duk abinda ya dace. Washe gari har ya fisu zumuɗin son fita ma, sauran da basu san miya faru ba canjawar Barrister ɗin taita basu mamaki.....      ★★... KAUYEN JUMNA ★★....     Tun kammala bayanin Abu Zainab ga su Kaka jikkunansu duk yay sanyi, Ummu ma hawaye takeyi, Barrister shine hope ɗin su a yanzu bayan UBANGIJI masanin abinda ke fili da ɓoye. Gashi a dalilinsu an rasashi. Idan har aka cutar da shi ta dalilinsu bazasu yafema kawunansu ba.          Kaka dai jinjina kai kawai yake amma komai ya kasa cewa, sai Iyyani ce cikin ƙarfin hali da sharar ƙwalla ta dubi Abu Zainab da damuwa ke shimfiɗe a fuskarsa. “Zakariyya kuyi haƙuri dan ALLAH, mun jefa rayuwarku a haɗari, ya ALLAH ka bayyana Abdullahi da gaggawa”.     Ɗan murmushin yaƙe Abu Zainab yayi, cikin danne abinda ke masa kaikawo yace, “A'a mama ai mutum baya taɓa wuce ƙaddararsa, kuma har yanzu bamu tabbatar ba ko akan wannan case ɗin bane muka rasa shin, dan Barrister da kike ganinsa nan shima hatsabibin kansa ne, gaskiyarsa da tsayuwa akan ganin tabbatar da ita yasa yanada maƙiya da yawa akan cases daban-daban hatta a cikin abokan aikinsa ma. Kinga kuwa zama ta iya yiwuwa ba'akan wannan ɗin bane.....”       “Dole ya zama akan wannan ne” Kaka ya faɗa cikin katse Abu Zainab. Duk kallonsu suka maida a kansa. Ya jinjina kai batare da ya kallesu ba. “Ban san gaibu ba, amma inaji a jikina akan su Muhammad Zayyanu ne, sai dai kuma tabbas koma a ina yake har yanzu yana raye insha ALLAHU. Inajin wannan ƙwarin gwiwar ne a zuciyata”.        Ba ƙaramin mamaki kalaman kakan suka basu ba, sai dai kowa ya gagara cewa komai sun dai zuba masa ido. Kusan mintuna biyu gidan shiru kafin kaka ya miƙe, babu jimawa ya dawo da jakka a hanunsa. Su dai duk suna kallonsa kawai. Takardar daya zaro ya miƙama Abu Zainab. “Ungo duba wannan”.      Da sauri Abu Zainab ya amsa ya fara karantawa. Bakinsa cike da magana ya ɗago yana duban kaka da ke kallonsa. “Baba wannan kuma fa?”.     Murmushi Kaka yayi da kauda kansa kamar bazaice komai ba. Sai kuma ya ɗan taɓe baki da fara basu labarin yanda duk a kai a randa zai dawo. Ya ɗora da faɗin, “Saurayin daya kawoni gidan nan zuciyata ta bani ba haka nan ya kawoni ba....”         “Amma baba shine ka amince harma da nuna masa gida?”.     Kaka yay ƴar dariyarsu ta manya. “Zakariyya kenan, to idan baka iya kama ɓarawo ba ai shi sai ya kamaka. Ka ganni nan barni kawai inda ka ganni. Idan na nuna nasan yanada manufa a kaina tun farko kamar yanda naso nuna masa a tasha ai bazan san sirrin zuciyarsa ba. Amma dana bashi dama fa? Yanzu a tafin hannuna yake, kuma jirace nake da zuwansa dan na tabbatar zai dawo, na masa talalar da tabbas sai ya dawo da izinin UBANGIJI”.          Abu Zainab kam a yau Kaka ya fara bashi tsoro. Sai dai ya danne bai yarda ya nuna ba. Kaka ma ya fahimci haka amma ya kanne, sai jakkar ya tura ma Abu Zainab yana faɗin, “Wannan sune kuɗin dake tare da takardar”.     Nan ma dai da mamaki Abu Zainab ke kallon kuɗin, kuɗine masu yawa sabbi ƙal sai ƙamshi suke na sabunta. “Baba waɗan nan mutanen kuwa anya....”          Kaka yay murmushi mai bayyana haƙora. Sai kuma ya ɗan kalli sashen da Ummu ke zaune. Tuni ta tashi batare da sun farga ba har Iyyani..........✍️ *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_46_* ..........Lokacin da kaka yayi ma Abu Zainab rakkiya sukejin halin da ƙasar ke ciki, dan shima Abu Zainab kasancewar fitowar sassafe yayi sannan komai bai fasu ba. Hankalinsu yayi matuƙar tashi dan basu san wacece a cikin matan sarkin ta rasu ba.       “Zakariyya zama bai ganni ba, dole ne mu wuce tare kenan, kayi haƙuri kaɗan jirani anan ina zuwa”.    Kaka bai jira cewar Abu Zainab ba ya koma gida da sauri, koda su Iyyani sukaga a yanayin da ya shigo suma hankalinsu ya tashi, amma tambayar duniya yaƙi ce musu komai kan abinda ya farun, sai cemusu da yay shima zaije Daular ruman ne.”. jin wannan furucin nasa yasa jikin Ummu fara rawa, a hankali ta zube ƙasa dan zuciyarta ta gama bata kodai ta rasa Iffah ko su Babiy. Dama yau kusan gabbanin asuba tayi mafarkin Iffah na kuka da kiranta tazo ta ceceta, sai kawai ma zuciyarta tafi karkata akan Uffan..          Su Kaka sun iso daular ruman a harmutse, dan ƴan zanga-zanga nata da ɗa karuwa harma abin na bama mutane mamaki. Yayinda jami'an tsaro tuni sun fito ta kowane titi na masarauta sun tare. Da ƙyar suka samu ƙarasawa gida, kasancewar ana aikowa gidan domin halartar jana'iza yasa Kaka yay tunanin wannan ma indai Iffahr ce zasu aiko. Dan haka suka shiga tambayar ƴan anguwa amma kowa na tabbatar musu babu wanda yazo. Hankalin Kaka ya tashi fiye da farko, dan kuwa dai bayan wannan hanyar babu wata mai sauƙi da zai iya ji sai abokinsa dogon yaro da ke cikin masarauta. A yanda kuma garin yake hakan abune mai wahala a garesa kenan......     ★ BARRISTER ★               Yanayin da aka wayi gari a ƙasar bai hana su Barrister fitowa ba, sai ma lokacin shi yasan abinda ke faruwar, al'amarin ya taɓa masa zuciya, dan ta wani fannin case ɗinsa tamkar kacokal yanada alaƙa mai ƙarfi ne da abinda ke faruwar. Har yaji yana tsoron ace yarinyar ce ma ta rasa ran nata. Dan dole dai ya daure ya isa inda ya nufa. A yau dai bai samu Sayyid Faizul-Anwar a falon ba, sai dai kasancewar an san da zuwansa ya samu tarbar data dace. Bayan zaman kusan mintuna arba'in Sayeed ya fito cikin shigar jallabiya, cikin girmamawa Barrister ya gaidashi, ya amsa masa da kulawa shima yana masa barka da zuwa. Suna tsaka da gaisuwar cikin yaran Sayeed ya shigo ya isar da saƙon zuwan wasu baƙin. Damar shigo da su ya bada dan yasan da zuwansu, daga haka ya maida hankalinsa kan Barrister.        Barrister yayi matuƙar mamakin ganin baƙin, sai dai ya danne hakan dalilin kallon da suke masa matsayin Barrister Akeem. Gaisuwa sukai ta mutunta juna, har suna tsokanarsa da cewa shine idonsu na gari. Murmushi yayi yana rissinar da kai alamar girmamawa. “Kar kuji komai ranka ya daɗe, a komai muna tare da ku kuma zamu kare mutuncin ku”.     Sosai suka nuna jin daɗi da zancensa. Nan suka shiga kwarzantashi. Shi dai nasa murmushi ne a zahiri, a kasan rai kuma yana matuƙar mamakin abokinsa da ɓoyayyun ayyukansa. Dan bai taɓa tunanin Barrister Akeem zai iya irin waɗan nan ayyuka ba.....      “Barriter ina alkawarin mu?”. Sayeed Faizul-Anwar ya katse masa tunani. Ajiyar zuciya yaja a ɓoye, sai kuma ya muskuta yana murmushi da taɓa bag ɗin daya shigo da ita. “Ranka ya daɗe komai yazo hannu fiye ma da yanda kuke buƙata. Sai dai kafin mukai ga nan ina son nace wani abu saboda wasu dalilai”.            “Faɗi kanka tsaye Barrister baka da damuwa akan hakan”.    “Nagode ranka ya daɗe. Bawani abu bane mai girma akan dai shi wannan case ɗinne. Komai dai gashi na gani anan kuma na tattaro, sai dai yanda aka bani aikin a dunƙule ina ganin ya kamata nace wani abu duk da dai naga komai a kansa, amma saboda nasan inda duk ya kamata na toshe a ramukan da zasu iya yunƙurin buɗewa koma su buɗe ɗin yasa nake son bada shawara bisa wani hangena”.      Shiru kamar bazasu ce komaiba. Sai dai sun maida dubansu ga Sayeed Faizul-Anwar, kai ya gyaɗa musu alamar tabbatar da babu matsala, dan haka kusan a tare suka sauke numfashi, kafin ɗaya a ciki ya shiga faɗin. “Barrister mun yarda da kai, sai dai ka sani koda baka san komai akan case ɗin nan ba bazamu taɓa bari wani rami a buɗe mana ba koya buɗe maka, zamu kasance a bayanka a kowanne lungu da saƙo na ƙasar nan.”        “Nagode da wannan karamci”. Barrister ya faɗa da girmamawa.    “Baka da damuwa Barrister ka cancanta ne.”         Murmushi ya sake saki tare da mikewa ya kai jakar gabansu, cike da farin ciki suka buɗe suna mai fiddo duk takardun ciki. Bayan sun ɗan dudduba su suka ɗago fuskoki cike da murmushi suna yabama Barrister namijin ƙoƙarin sa. Shi dai nashi murmushi ne kawai. Ɗaya daga cikin baƙin da ake kira da Sayeed Harun Al-rashid, babban mutum ne a ƙasar ta ruman, dan riƙƙaƙen ɗan kasuwa ne na gwal da kowa ya sani kasancewar sunansa yayi matuƙar shura a wannan harkar data zama babban tattalin arzikin su na ƙasar, dan Ruman kam bata san iya arziƙin gwal da ALLAH yay mata ba, shiyyasa duk wani riƙƙaƙen ɗan kasuwa zaka samu gwal ɗin ne mafi rinjayen makaminsa kamar dai Sayeed Harun Al-rashid. Ta wani gefen kuma yana riƙe da sarauta sai dai yafi bama kasuwancin muhimmanci matuƙa. Zamansa ya gyara sosai yana fuskantar Barrister. “Barrister yanzu mi kake son ka sani?”.      “Ranka ya daɗe ba komai bane dama sai akan waɗan da naga case ɗin ya karkata. Na duba dukkan bayanan Barrister Abdallah Aas, sai dai a yanda na fahimta kamar ya gano inda su mutanen dake hannun naku suke, dan kafin ma ya rasa ransa kamar ya fito da ga ƙauyen Lufana ne wajen matar marigayin, abinda nake son cewa anan ina tsoron yazam bayan Barrister ɗin akwai wanda yasan wannan sirrin. In kuwa hakan ta kasance zaman mutanen a station ɗin dana fahimci kun ɓoyesu zai zama barazana ke nan koda anan gaba”.     Kusan a tare sukai murmushi, Sayeed Harun Al-rashid ya muskuta zamansa cikin nuna damuwa da zancen Barrister. “Maganar ka nakan hanya Barrister shiyyasa tun kafin yau muka gama maganin duk abinda kake gudun. Tun daga farkon wannan case ɗin idanunmu akan komai suke, dan haka ka kwantar da hankalinka. Su kuma tuni basa a police station ɗin, dama mun kai ajiyar su ne domin ɓadda kama bayan kwanaki kuma muka ɗauke su, amma kai a yanzu mi kake son cewa?”.     Anzo dai-dai gaɓar da Barrister keson azo, dan haka ya ɗan murmusa yana mai ƙara bama kansa nutsuwa. “Alhmdullh kun fahimci inda nake buƙatar akai ranka ya daɗe. Abinda nake son cewa kai tsaye shine ayi duk yanda za'ai cikin kwanaki biyun nan abar ƙasar ruman da mutanen gaba ɗaya”.         “Eh maganarka abin dubawa ce kam, amma kuma mizai hana kawai a ɓaddasu a wuce wajen, dan abinda ya zama dalilin zuwansu hanunmun ma an sameshi cikin sauƙi yanzu haka”.     Barrister yay ɗan jimm dan bai fahimta ba, amma sai ya dake bai sake musu wata tambaya ba gudun karsu zargi wani abu. Sai dai ya cigaba da faɗin, “Ɓaddasu bashine mafitaba ranka ya daɗe, dan a ɗan bincike da nayifa akwai babbar matsala game da mutuwar Barrister Aas”.       Babu wanda zancen bai daka ba a acikinsu, Sayeed Faizul-Anwar daya kafe Barrister da ido yay saurin faɗin, “Barrister bamu fahimce ka ba, mi kake son cewa?”            “Ranka ya daɗe yanzu zan fahimtar da ku. Idan har kun saurari dukkan labaran dake yawo har yanzu babu wani tabbaci na samun alamar sassan mutum a cikin motar Abdallah, wannan shine yaja hankalina tun a ranar farko bayan nabar nan na fara nazari da bincike. Tabbas Abdallah na raye, sai dai ya ɓoye kansa domin bada ƙafa. Na sanshi nasan mizai iya fiye da tunaninku. Shiyyasa nake ganin kashe mutanen a yanzu bashine mafita ba, muyi nesa da su da ƙasar nan ta yanda babu inda zasuji ɗuriyarmu, sai kuma mu samo wasu a madadinsu a buɗe shari'ar ta yanda zamu ƙona Barrister Abdallah Aas da ransa batare daya farga ba”.         Dukansu gumi suke na tashin hanakali, sai dai babu wanda ya iya cewa komai har zuwa wani tsahon lokaci. Sayeed Harun Al-rashid ya nisa yana mai share ɗan gumin daya taru masa a goshi. Ƙyaƙyƙyawar fuskarsa fara tas gaba ɗaya ta ƙwaɓe alamar rashin damuwa. “Zartar da hukunci bazai yuwu yanzu ba Barrister, amma kaje zuwa anjima zakaji komai ta waya”.      “Babu damuwa ranka ya daɗe”. Barrister ya faɗa cikin jimami shima, sai dai acan ƙasan ransa dariya yakeyi, yayinda wani gefe na zuciyarsa ke tabbatar masa akwai wani babba mai alaƙa da case ɗin bayan su, shiyyasa bazasu iya zartar da hukuncin ba kai tsaye. Yau ma dai an rakosa da kuɗi masu yawa har mota.......                 ★★... BAYAN KWANA BIYU ★★....      A kwanaki biyun nan abubuwa da yawa sun faru tako wane ɓangare, sai dai marasa daɗi sunfi masu daɗin rinjaye. Zuwa yanzu dai da gaske ƙasar ruman da jama'arta suke basa buƙatar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed matsayin Shahan-shan. Dan tun tsirarun mutane na zanga-zanga a wasu jahohi takai yanzu ƙasar ma gaba ɗaya ta ɗauka. Abu mafi ban mamaki harda wasu a manyan ƙasar na nuna goyon baya ga talakawa, ciki kuwa harda wasu Tajwar na jihohi. Yayinda ta wani gefen kuma hankalin wasu manyan ƙasashen duniya ya fara dawowa kan zanga-zangar dama dalilin yinta.       Babban abinda ke tunzura jama'a shine biris daga Shahan-shan, yayinda kuma a cikin gida hankalin ƴan majalissar sa ya rabu kaso biyu, wasu na goyen bayan ya saukan wasu na buƙatar karya sauka dan shine kawai ya cancanta da kujerar a ganinsu. A talakawan ma bai rasa tsirarun masoya ba, sai dai basu da ƙarfin ja da masu boren shiyyasa suka koma gefe sukai shiru matsayin masu kallo da ido.      *_IFFAH!_*       A kwanaki biyun nan yanda Daular ruman ke a hargitse haka Iffah ke a hargitse. Kuka kam idanunta har sun daina fidda ruwan hawaye. Cikin ƙanƙanin lokaci tayi wata irin rama mai ban tausayi. Haukan da iyalan Sayeed Khairul-Bashar keyi a masarautar da wanda jama'a keyi a waje sai ta ɗaukesa wasan yara. Idan su da suka rasa uba kawai zasu harmutsa masarautar haka ina ga ita data rasa ahalinta duka, a ganinta ita ya cancanci ta hargitse ƙasar ruman baki ɗaya ma ai. Sai dai yanda ƴan zanga-zanga ke daɗa ƙaruwa na saka mata farin ciki, dan abin ban mamaki har wasu a cikin Tajwar na jihohi suma sun ƙara tunzura wuta da bada goyon baya akan saukar Shahan-shan ɗin, hankalin ƙasashe kuma ya fara dawowa ƙasar ruman, da alama dai dama a jirace kowa yake da wannan damar. Hakan na sake tunzura ƙwarin gwiwar ƙudirinta.       Wutar wannan al'amari na ƙara ruruwane dalilin shirun Tajwar Eshaan. Babu shi babu cewarsa, harma wasu sun fara tunanin anya kuwa yana cikin masarautar ma ko?.... Duk wannan bai damu Iffah ba a yanzu, hankalinta gaba ɗaya ya tattara ne akan ta ina zata samo dafin maciji. Bata da wani amintacce a cikin masarautar, a waje kam sir Fawzan ne kawai, shima kuma zuwa yanzu ta fara shakku akansa saboda tana ganin ya ɓoye mata abinda ya faru da su Babiy ne bisa wata manufa. Idan tace zata fita a sulale daga masarautar taya kuma zata dawo cikinta? Wannan ƙalubalen keta faman mata kaikawo harya gagara samun mafita a kwanaki biyun nan. Tana a bangarenta bata ganin kowa kowa baya ganinta, waɗan da zasu iya ganinta hankalinsu a tashe yake dan kai tsaye su abin ya shafa, shirunsu kuma sai ya bama Iffah damar fassarashi da abinda zuciyarta ta gama tabbatar mata, dan haka itama a yanzu ta haƙƙaƙe bata da lokacinsu.               Kamar yanda ta tsara bayan sallar la'asar ta shirya tsaf cikin abaya data amshi jikinta, dan ma ta rame ga idanunta da suka ɗan kuklumburo amalar taci kuka bana wasa ba. Duk da masarautar a harmutse take haka ta keta cikinta hadimanta na take mata baya har sashen marigayi Sayeed Khairul-Bashar. Tayi matuƙar mamakin tarbar data samu dan batai zaton irinta ba, sai dai abinda bata sani ba shine su kallon tausayi suke mata da tabbatar da itama bawai ta tsira bane a hannun azzalumin. Dan malamin duba da matar Sayeed Khairul-Bashar ɗin ta ziyarta tun lokacin daya ɓata kafin aga gawarsa ya tabbatar mata akwai ƙulli mai girma da Shahan-shan keyi game da rayuwar Iffah shiyyasa itama bata mutu ba a sanda aka kaita sashenshi. A ranar bata ɓoyema ƴaƴanta komai akan zancen nan data jiyo ba, sun kuma yi niyyar samun Iffah har sashenta da batun washe gari aka tashi da wannan tashin hankali. Wannan shine dalilinsu na mata tarbar data bata mamaki. Ita kuma kasancewar zuciyarta a kusa take tana musu ta'aziyya tana share hawaye da handkherciff. Sai hakan ya ƙara mata kima a idon iyalansa. Yayinda ƴan uwansu kuma da basu san komai na ke jin zafin ganin Iffahr da fassarashi matsayin leƙen wani asiri dan a yanzu wasu a cikin ahalin masarautar su kuma suna ma Iffah kallon wata ƴar kaɗafin Tajwar Eshaan ce tunda har ta tsira daga kisan gillarsa..........✍️               *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_47_* .........Kamar yanda Iffah tai tunani labarin zuwanta sashen Sayeed Khairul-Bashar ta'aziyya har ya isa kunnen surukarta dama na jikin Tajwar Eshaan irinsu malikat Haseenat da su Daneen Ammarah. Dan tana fitowa kiran Daneen Ammarah ya shigo wayarta. Bata ɗaga ba, aka kuma sake kira nan ma dai ta share kamar bataji ba. Sai da ta koma sashenta da kusan mintuna goma sannan tai kiran Daneen Ammarah ɗin back. A bugu biyu ta ɗaga, Iffah ta taɓe baki cikin rashin damuwa tai sallama da fara gaishe ta. Da kulawa Daneen Ammarah ta amsa. Iffah na jiran jin ta mata batun fitarta sai Daneen Ammarah ta jeho mata tambayar da bata da alaƙa ma da fitar.         “Ibnati na kiraki ne akan Abni, shirunsa na tadamin hankali matuƙa, gashi yana ƙara harzuƙa mutane ƙasa, kinga dai yanda ƙasar nan ke sake rikicewa. Mu dukanmu mun nemesa a waya amma bamata shiga, na fara zargin anya ma yana cikin masarautar nan?”.      Murmushin takaici Iffah tayi, amma a zahiri sai ta danne ta fara magana cikin kwantar da murya. “Wannan shine tunani na nima Mamy, sai dai ban san yanda zanyi ba ganin ku manya bakuce komai ba.”          “Shirun na dole ne Ibnati, bazaki gane babbar sarƙaƙiyar dake cikin masarautar nan ba ne. Amma tabbas akwai matsala, akwai kuma gagarumin al'amarin dake ɓoye amma yana son bayyana kansa a wannan gaɓar.....”     Cikin zumuɗi Iffah tace, “Mamy minene shi dan ALLAH?”.    “Humm Fareedah kinyi ƙarama da yawa ba yanzu ba. Ke dai kawai abinda nake so da ke shine ki taimaka ki bincika min idan Abni yana a gidan nan...”           “To Mamy, amma dai zaiyi wuya tunda kunce idan yana cikin damuwa kulle kansa yakeyi baya kuma sauraren kowa. Sai nake ganin ni taya zai saurare ni”.      Murmushi Daneen Ammarah tayi mai sauti. “Rashin saurarenmu bashi ke nufin kema bazai saurareki ba Ibnati. Ke dai gwada sa'arki mu gani”.     Iffah dai ta jita ne kawai, amma sai bata sake musawa ba sukai sallama.....       ★★.... ★.....    Miran Jasim ya sauke wayar dake a kunnensa bayan gama sauraren abokin wayar tasa, yanda fuskarsa ta canja daga farin cikin dake shimfiɗe a kanta kafin wayar yasa Miran Arshaan sake maida hankalinsa garesa. “Wani abu ya sake faruwa ne?”.       “Zai dai faru”. Cewar Miran Jasim ɗin a fusace yana miƙewa. Miran Arshaan da maganar ta dakesa ya miƙe zumbur shima. “Ban gane mi kake son cewa ba Jasim Akh?”.      Kamar bazai tanka masa ba sai kuma yaja kakkauran tsaki. “Harun Al-rashid ne dai akan waccan maganar banzar ta ranar, duk yabi ya tashi hankalinsa yana cigaba da damuna nima, tun abin bai tasiri a raina ba har ya fara, wai Barrister da suka bama aikin can kan ɗan iskan can ne ke cigaba da musu bayani dai kan Barrister Abdallah bai mutu ba dai da gaske.”         “Wai suna nufin shi ya tabbatar da hakan kenan?”.      “Abinda ke cazamun kai kenan, na rasa wane shirme ne kuma hakan? Taya wanda bomb ya tashi da shi ace bai mutu ba?”.    “To amma fa kuma maganarsu fa abin a duba ce Jasim Akh. Dan koni naji shakku a randa bomb ɗin nan ya tashi amma jami'an tsaro suka tabbatar babu wani alamar an rasa rai......”        “Amma shine kai shiru?!”. Miran Jasim ya katsesa a zafafe. “Mi kake so nayi bayan wanda nayi to? ina son ka tuna tun a ranar na kawo maka wannan zancen amma ka nuna min cewar zata iya yuwuwa ƙarfin tashin nakiyar ya cillashi wani waje ne shiyyasa basu gansa ba. A kuma shekaran jiya da suka kawo maganar na kuma ƙoƙarin maka nuni ka kalli zancensu a shirme”. Shima Miran Arshaan ɗin ya karɓa masa a nasa zafin.     Shiru Miran Jasim yayi da dafe kansa yana murza goshinsa dan ya tuna tabbas anyi hakan. Amma wannan aikin na cikin gida da rashin sanin mi Tajwar Eshaan ke ciki ya ɗauke hankalinsa bai nutsu yayi nazari kan batunba kasancewar akwai abubuwa da yawa da bawai yana buɗema Miran Arshaan ɗin bane, kamar yanda shima Miran Arshaan ɗin ba komai yake yarda ya buɗe ma Miran Jasim ɗin ba. Sai dai a yanzu dukansu sun fahimci yin kuskure, dan haka kowanne ya ajiye ɓoyayyar manufarsa suka fuskanci juna.           “Ni ina ganin in har an yarda da aikin Barrister ɗin nan shawararsa ba abar yardawa bace. Sannan dole ne fa mu gaggauta ganawa da yarinyar can in ba hakaba aikinmu zai iya buɗewa. Dan idan ya kasance Barrister Aas na raye bazai samu ɗaki bane ya kulle kansa domin hutu kaima ka sani”.      Miran Jasim ya gyaɗa kai da faɗin, “Hakane maganarka na kan gaskiya. Yanzu minene abinyi?”.     “Abinyi ɗaya ne bama Barrister Akeem damar shigewa gaba kafin kwana biyun nan na cikar aikinmu abar ƙasar nan da mutanen. Bayan ka haye karagar mulki shi kuma shegen duk inda yake zamu nemishi ne ya ɗan-ɗana kuɗarsa”.      “Ina sake godema ALLAH da kasancewar ka kusa da ni, dan kana farkar da ni a duk sanda kaina ya shiga duhuwa ɗan uwana”.     Murmushi Miran Arshaan ya saki a zahiri, a zuciya kam faɗi yake, (Banza ka gama cusamin ƙayar a rumbu na rufeta da ɗan boto ina daga kwance).     Ɗaukar wayar Miran Jasim dai-dai da kammala wayar Iffah da Daneen Ammarah daga can......        ★★.....      Tana ajiye wayar wani kiran ya sake shigowa, kamar zata share dan bata san number ɗin ba sai kuma dai ta ɗauka da tunanin ko Sir Ajmaal ne kasancewar a saƙonta na ƙarshe ta roƙesa idan ya gani ya kirata. Daga can aka amsa sallamarta kai tsaye, hakan ya sata Ciro wayar a kunenta ta kalla tamkar mai son gano muryar. Miran Jasim da kamar yana ganinta yay gyaran murya, hakan ya sata sake maida wayar.      “Kina magana da Jasim Ibn Abdull-Majeed Aliy”.    Kai tsaye Iffah ta ganesa, dan haka ta fara gaidashi da girmamawa. Hakan ya masa daɗi, dan yanda yake amsa mata da kulawa zai baka tabbaci. Shiru ne ya ɗan biyo bayan gaisuwar, kafin ya katsesa da faɗin, “Ibnati inata zaman jiran ji daga gareki amma shiru. Ko baki amince da abinda kika gani bane ba dai?”.         Iffah da ke jin an taɓo mata inda ke mata ƙaiƙayi hawaye suka shiga rige-rigen sakko mata. Hannu tasa ta sharesu da ɗan jan hanci. “Ba yarda ne banyiba ranka ya daɗe, kawai dai zuciyata na kaikawo ne na son sanin dalilinka na yin hakan a gareni. Idan ban manta ba kai fa Ammi ne garesa, mizaisa ka zaɓeni sama da shi? A barshi ma zaka iya hakan kasancewar ka mai gaskiya ko ƙyamar abinda yake. Amma miyasa su na baya da aka rasa bakuyi wani yunƙuri ba sai ni a kaina bayan akwai ƴaƴan Tajwar mafi rinjaye a cikin wanda ya halaka?”.      (Kaga ibilishiyar yarinya) ya ayyana a zuciyarsa. A zahiri kam sai yay gyaran murya cike da dattako yana kallon Miran Arshaan da shima ke sauraren komai. “Wato Ibnati duk yanda zan miki bayani a wayar nan ba lallai ki fahimta ba. Amma zan tura miki lokaci da adireshi mu haɗu zai fi”.           Jimmm Iffah tayi kamar mai shakku, sai kuma ta nisa cikin gyaɗa kai tace, “Okay babu damuwa ina jira”. Daga haka sukai sallama kowa ransa na masa kaikawo...       ★★....     Cikin ƴar dariya Miran Arshaan yace, “Amma shegiyar yarinyar nan fa da zata samu dama a masarautar nan ba ƙaramin hatsabibiya za'ai ba. Kaji murya cauy-cauy bata ko tsallaken kalma ga shegen wayo”.        “Shiyyasa dolene tana kammala aikin nan a kaudata kawai, ai tunda har tana da ƙarfin halin shigowa masarautar nan da ƙudiri irin na kashe Shahan-shan dama nasan zamuga fiye da hakan tattare da ita. Irin waɗan nan yaran masu taurin zuciya a cikin mata basu da yawa, amma kuma kasancewar su mata ga mai mulki ba karamin ƙara samun power bane. Badan-badan ba babu abinda zai hanani tabbatar da ita abokiyar tafiyata. Dama yarinyar ga shegen ƙyau da ƙira tamkar ita ta zana kanta...”       Ƙaramar dariya Miran Arshaan yay idonsa akan ɗan uwan nasa. “Wato dai Jasim Akh har yanzu bazaka canja ba, na ɗauka tuni ka jingine batun son matan nan naka kodan kujerar da ke gab da zama taka”.          “Bazaka gane bane Arshaan Akh”. Miran Jasim ya faɗa yana tasa ƴar dariyar shima da komawa jikin kujera ya lafe ƙyaƙyƙyawar surar Iffah da bata wuce sa'ar autarsa ba na masa kaikawo. Shima dai Miran Arshaan ɗin hakance a ransa, dan tun randa suka haɗu da Iffah a wajen wasan takobi da Tajwar Eshaan yarinyar ta kasa barin ransa. Duk da dai shi yanzu kam ya ɗan rage bin mata tun aurensa da Jasrah.      Humm masu karatu Bara na ɗan tsakura muku wata gulma dai karna wuce. (A baya ƙiyayyar ƴan ɗakin su Miran Jasim da Miran Arshaan a bayyane take fiye data ƴan ɗakinsu Tajwar Haysam (mahaifin Tajwar Eshaan kenan) amma a wasu shekaru bayan hawa mulkin Tajwar Haysam sai aka wayi gari sun ɗinke, ƙiyayyar da sukema juna ta koma ta ƙarƙashin ƙasa. Wannan haɗin kai nasu kuwa ya samo asaline a dalilin kasancewar halinsu da yazo ɗaya. Awani lokacin bikin al'ada kamar yanda duk suka saba sun baza yaransu samo musu yara matasan ƴammata masu jini a jika da basu gaza sha bakwai zuwa ashirin ba. Karku ɗauka da yardar yaran wai ake kai musu su, ko ɗaya, ta karfin tsiya za'a ɗaukeki bayan an shaƙa miki abu ko an yaudareki, bazaki tashi tsintar kanki ba sai a ɓoyayyen gurin da in zaki kwana dubu ihu babu mai jinki. Idan sun gama lalata rayuwar yaran kuma a jefar da su. Alokacin da labarin yaje ga Tajwar Haysam hankalinsa ya tashi, dan a shekarar an samu gawar yara ƴammata kusan biyar da waɗan da aka jikata, iya bincike kuma na jami'an tsaro ba'a sami komai ba. Da shekara ta dawo kuwa yasa tsatstsauran tsaro akan kaikawon mata fiye da maza, aka kuma sake sabon tsarin yanda bikin al'ada zai kasance. Ransu Miran Jasim ya ɓaci matuƙa, dan ƙarshe sai a yaran masarauta suka huce haushinsu ƴaƴan talakawa sun gagara ɗauka. Duk da ba tare suke aikatawa ba sai shirunsu yazo ɗaya a lokacin, har ya kasance yaransu dake sato musu ƴammatan sunyi haɗaka akan yarinya rigima ta kaure, kowanne ya sanarma ogansa, a zafafe Miran Jasim da Miran Jasim suka buƙaci sanin juna kowanne da tunanin shike da ƙarfin iko, sunko haɗun a yanayin da hantar kowanne ta kaɗu dan mamaki, amma ƙwallafa rai da kowannensu yayi akan yarinyar ya sasu amincewa juna yin tarayya da ita a tare Wa'iyazubillah 😭🤦. Haka suka haɗu suka lalata rayuwar yarinyar daga ƙarshe ta rasa ranta, a cikin masarautar suka bizneta har a yau kuma babu wanda ya san hakan sai ɗauka da ake yarinyar ta ɓata ne a taron bikin al'ada. Wannan shine sanadin zamowarsu inuwa ɗaya dan wannan ya basu ƙofar dinga kawoma juna mata, sai dai Miran Jasim yafi Miran Arshaan ƙwarewa a harkar, dan shi har order mata yomasa ake daga wasu ƙasashen ma🤦). Wanda ya gane na tayasa murna, wanda bai ganeba ya tsallake kawai😂🥱.              ★★ BARRISTER ★★       Kamar yanda su Barrister ke zaman tsammani a yau sai ga kira daga Sayeed Harun Al-rashid, sun tattauna sosai ciki harda yarjewar fita da su Babiy zuwa wata ƙasa da kuma tsananta bincike wajen gani maɓoyar Barrister Abdallah Aas kamar yanda Barrister suka tsara musu. Abu mafi saka Barrister a ƙololuwar farin ciki shine damƙa fita da su Babiy ɗin a hannunsa, amma a zahiri sai ya nuna hakan ba aikinsa bane, shifa ya bada shawara ne kawai.           A ɓangaren su sun nuna masa sufa sun yarda da shine, bayan shi kuma bazasu iya bama wani aikin ba gudun abinda zai je ya dawo. Bayan dai ɗan cigaba da tirjewa da ga ƙarshe Barrister ya amsa. Hakan ya musu daɗi suma, dan a nasu ɓangaren sun bashi aikinne domin ƙullama rayuwarsa, acewarsu koda ta tashi salin alin zasu zare hanunsu su barsa a ciki.         Barrister da ya gama fahimtar su da ƙudirinsu duk da basu fito sun faɗa ba yay murmushi yana mai girgiza kansa da mamakin mutanen wannan duniya mai cike da rikici.  “Son kai shine tushen rugujewar kawunan mu a wannan duniyar. Mai mulki kansa kawai ya sani. Mai arziƙi kansa kawai ya sani. Talaka kansa kawai ya sani. Mai ilimi kansa kawai ya sani. Jahili kansa kawai ya sani. Iyaye kansu kawai suka sani. Matasa kansu kawai suka sani. Yaro kansa kawai ya sani. Kowa akan buƙatarsa kansa kawai yake iya kallo. Duk shaƙuwa irin ta ma'aurata akan son kansu kowanne zai iya aikata komai. Duk shaƙuwa irin ta ɗa da iyaye akan son kansu zasu iya komai. A wannan duniyar yanzu samun cikakken amini sai an tona, ka gama yarda da mutum amma akan son kansa zai iya komai. Son kai dai! Son kai dai ya rabbi. Ƴan uwa son kai fa na kawo abubuwa da yawan gaske. Yana gina hassada a zuciya, ƙyashi, zalunci, raunana imani, ƙarya, munafunci, kai komai ma wlhy, hatta shirka tana iya shiga a cikin son kai batare da mun sani ba. Ya rabbi ka ganar damu gaskiya tun kan ta nisanta a kunnuwanmu da idanunmu.......✍️        (Wannan zance haka yake Barrister, ALLAH dai ka shiryar damu🤦).       *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_48_* ...........Babu kwanciyar hankali gasu Kaka, dan har yanzu basu sami bakin zaren jin komai ba game da wadda aka rasa a cikin matan Shahan-shan. Ga tashin hankalin ɓatan Barrister dan sun je har gidansa amma a rufe alamar iyalansa ma dai basa nan. Acewar makwafta kuma dai anzo an kwashesune a cikin dare, yau kusan kwanaki takwas kenan. A lissafinsu kuma ya kama randa Barrister ya ɓata kenan. Zuciyar kaka ingizashi take kan abubuwa masu yawan gaske amma yana gocewa, dan duk tsanani yayi alƙawarin dogaro ga ALLAH majiɓincin al'amuran bayi a kowane tsanani da sauƙi. Kwanansa ɗaya ya juya ƙauyen Jumna, dan yasan ya baro su Iyyani a tashin hankali.       Ilai kuwa koda ya koma sai ya samesu a birkice, dan suma dai zuwa yanzu labarin halin da ƙasar ke ciki ya isa har kunnuwansu. Ummu tayi kuka har hawaye sun daina zuba. Ta gama sadakarwa ta rasa autarta itama. Dama ta jima da fidda rai ga su Babiy tuni. Kaka rasa ma mizai ce da su yayi, dan shima dai nasa kan a zafafe yake. Sai kawai ya shige ɗakinsa ya rufe kansa yana mai safa da marwa.......           ★★..... BARRISTER ★★......     Da taimakon masu tsaronsa bisa umarnin ogansu da tun a ganin farko da yay masa bai sake ganinsa ba sai ta waya tun a yammacin ranar suka fara tattara abubuwan da zai basu kariya wajen fita da su Babiy duk da basu zo hanunsu ba har yanzu. Sai dai a daren ranar su Sayeed Harun Al-rashid sukai alkawarin danƙasu hannun Barrister, duk da ya nuna musu shifa yana jin tsoro su bari komai ya kammala sannan suka nuna masa suna tare da shi da kuma tsaro na musamman duk da kuwa ƙarya ne a baɗini.          Zancen kam nasu ya tabbata, dan a daren ranar ƙarfe kusan tara na dare aka damƙa Babiy da Hanash a hannun Barrister Abdallah Aas matsayin Barrister Akeem da zukatansu su suka ɗauka. Daga gani kasan sun jigata matuƙa, sun rame sosai sunyi duhu. Ga rashin ƙarfin jiki da zaman waje ɗaya harma da ƙarancin abinci dana iska mai ƙyau. Hankalin Barrister ya tashi matuƙa, ya dinga share hawayen tausayinsu. Ya sake tabbatar da mutanen nan da suka kamashi mutanen kirki ne a yau, dan ana iso da su Babiy hanunsu sai ga likitoci, dan-da-nan suka duƙufa kansu da kulawa kai kace dama a shirye suke da hakan.......          ★★..... MASARAUTA ★★.....    Duk da ƙarancin shekarunta ALLAH ya bata basira irinta masu hangen nesa. Tun bayan gama wayarta da Miran Jasim zuciyarta bata aminta da yarda su gana fuska da fuska ba. Dan haka ana idar da sallar magrib ta tura masa saƙo kamar haka duk da ita ba sallar zatai ba tana fashi.       _Na amince mu tattauna, sai dai bata haɗuwa ba, muyi magana ta video call._      Miran Jasim ya karanta saƙon yafi sau ashirin, takaici kam ba'a magana ga ɗunbin mamakin basirar ƴar ficikar yarinyar. A take ransa duk ya jagule, ga boka Barbushi ya tabbatar masa haɗuwa da yarinyar fuska da fuska yafi fa'ida. Dan kwarjininsa da suddabaran da ya basu zai sakamata tsoronsa mai tsanani ya dinga yanda yaso da ita har zuwa sanda itama zasu ɓaddata bayan ta cika musu aikinsu. Gashi yanzu guri ya ƙure, bazai yiwu masa ba zuwa ga Barbushi ɗin dan zai iya rasa wannan damar da bokan nasu ya tabbatar musu itace ranarsu mafi Sa'a akan yarinyar kasancewar tana fashin salla, tana kuma cikin ruɗanin da ba komai yake iya banbancewa yanda ya kamata ba zasu iya sarrafata a duk yanda sukaso musamman akan Shahan-shan. Duk da sallar isha'i data gama gabatowa haka ya miƙe ya fice a masallacin bayan yayma Miran Arshaan alama da ido. Bai jima da fita ba kuwa yabi bayansa....        “ALLAH yasa dai lafiya na ganka duk a wani birkice?”.     Miran Jasim ya sauke idonsa akan Miran Arshaan mai maganar yana mai jan tsaki. “Wane kwanciyar hankaline da ni inba gani nai komai ya daidaita ba Arshaan. Yanzu ma ƴar iskar yarinyar nan ce wai fa ta turamin text message bata yarda mu haɗu fuska da fuska ba sai dai video call”.           “What! Waini wace irin hatsabibiyar yarinya ce wannan? Nama fahimci kallon sa'aninta take mana”.     “Ka barta karka damu, zata yabama aya zaƙinta ta dai gama mana aikinmu. Anan zata gane ko wanda ya ajiyeta a gidan bai isa ba balle ita karamar halitta. Ni yanzu damuwata ma shine Barbushi ya tabbar mana da wannan ranar ta sa'a, haɗuwarmu kuma fuska da fuska wani babban cigabane garemu.”             “Komai ya kwaɓe kam, sai dai ni a wannan gaɓar ina masa kallon mai sauƙi. Kaga dai a yanzu bamu da isashen lokacin komawa wajen Barbushi, na biyu barin wannan damar ta wuce a garemu kuskure ne. Dan haka kawai mubita a yanda take so ɗin, da sassafe mu nufi Barbushi”.     Ajiyar zuciya mai nauyi Miran Jasim ya sauke domin gamsuwa da zancen Miran Arshaan ɗin, daga haka basu koma masallacin ba sukai zaman kulla yanda zasu tunkari Iffah bayan sun tura mata saƙon amincewa ayi video call ɗin.    *_10:30pm_*         Ƙarfe goma da rabi na dare agogon ƙasar Iffah zaune gaban laptop ɗin ta, sanye take cikin suturar ta mai sirrinta jiki, iya zagayen ƙyaƙykywar fuskarta kawai ake iya gani. Tayi fayau ga mai kallo baka iya ganin komai sai damuwa da tsantsar ƙuruciyarta. Cikin girmamawa ta gaida dattijan guda biyu dake a fuskar lap-top ɗin tata. Miran Jasim da Miran Arshaan suka amsa mata da kulawa da nuna tausayawa tsantsa a fuskokinsu. Ita dai idanunta a rissine, dan tun kallo ɗaya datai musu bata sake yarda ta ƙara ba.       Miran Jasim yay ƴar gyaran murya da fara magana bayan gaisuwar tasu. “Ibnati mu mun sauke nauyin dake kammu naki, abinda kika yanke kawai muke buƙatar ji domin tsallakar da rayuwarki data ƴan baya. Dan a yanzu mun shirya tsaf ba tsafi ba ko bataliyar ifiritai Eshaan zai sauke a kammu domin danne cewarmu bazamu taɓa yin shiru ba”.          Iffah ta jinjina kai a hankali da faɗin, “Uncles naji daɗin hakan, kuma tun farko dama haka ya kamata ku kasance, duk da dai nasan bai zama lallai kuji irin zafin da iyayenmu sukaji ba. Amma a yanzu daya fara taɓaku gashi kun zaburo. Duk da haka bazamu ƙi karɓar taimakonku ba, dan a yanzu bani da wani abu dana tsana sama da shi, a shirye nake kuma na zama ajalinsa koda nima zan rasa nawa ranne. Sai dai ina son dan ALLAH uncle ka faɗamin gaskiya taya ka samu wannan videon? Ta ya kuma kasan na cikin videon nada alaƙa da ni ne? Miyasa kuke son taimaka mini? Miyasa duk da kun san yana kan rashin dai-dai baku taɓa wani yunƙuri ba a baya sai yanzu?”.       Kallon juna Miran Arshaan da Miran Jasim sukai kowanne ransa na susa da mamakin tsaurin idon wannan yarinya da sukema kallon hatsabibiya. Amma a zahiri sai Miran Jasim yaja ajiyar zuciya ya fesar cikin ƙoƙarin danne razanin da tambayoyinta suke neman jefasa. “Ibnati duk wannan ai na abin mamaki bane da har zai saka miki shakku, amma tunda kina son sani yanzu zakiji komai. Wannan video ɗin da kike gani na samosa ne a system ɗin Eshaan, bakuna shi kaɗai bane ba. Akwai ire-irensa da yawa harma dana yanda aka hallaka matansa na baya. Ina haɗasu ne domin miƙasa kotu a kwatarma masu hakki hakkinsu duk da ina fargabar ƙarfin iko irin na Shahan-shan bazai bari a hukunta shin ba kasancewar komai sai da say ɗinsa ke gudana a ƙasar ruman baki ɗaya. Sanin alaƙarki da wannan video kuwa ta samune duk a dalilin bibiyar tasa, sai dai bamu tabbatar ke bace ba sai a ranar da kika samesa tare da Arshaan Akh suna wasan takkubba. Sannan kasa tunkararsa a baya Ibnati bazaki gane ba, ƙarfin ikon Shahan-shan fa bana wasa bane ga kowa....”       “Tabbas hakane” Miran Arshaan ya amshe zancen. Batare daya jira cewar Iffah ba ya cigaba da faɗin, “Idan baki manta ba bayan kin basa shayi ya koma gefene yana kallo cikin masarauta, nima kina bani kuma na koma kusa da shi ina mai yabama tarbiyyarki da tabbatar masa yayi dace mace tagari data dace da shi a yanzu. Buɗar bakinsa sai ya sake tsaki da faɗin, “Tukunna dai, ai shi har yanzu matar da zai rayu da ita bata iso ba. Naji mamaki harna tambayesa ba'asin hakan amma sai bai tankani ba kin sanshi da girman kai. Zancen ya tsaya min a rai nazo na sami Jasim Akh da maganar, shine fa ya duƙufa bincike harya samu ganawa da kakanki da ke a ƙauyen Jumna”.         Sosai Iffah ta zabura da jin sun gana da kaka harta ɗago ido ta na kallonsu. Tabbas sihiri gaskiya ne, kuma yakanci kowama tunda har yaci ma'aikin ALLAH. A take wani abu mai sanyi ya dinga shiga jikin Iffah tamkar ana kwararashi cikin jininta. Hawaye ne suka silalo a idonta ta buɗe baki a hankali ta furta “Tabbas zan kashesa da hannuna, zan kashesa da dafin maciji na gaskiya kamar yanda yake halaka mutane dana tsafi. Nayi alkawarin yanda ya wargaza min ahali nima sai na wargaza rayuwarsa..”      Miran Arshaan da Miran Jasim suka kalli juna sukai murmushi. “Zako mu baki dukkan gudunmawar da kike buƙata Ibnati. Tare da kariya ta musamman ga duk wanda zai iya kawo miki hari, balle ma a yanzu abinda zakiyi sai dai ya ƙara kawo miki ɗaukaka dan irinki ƙasar ruman ke nema. Mi kike buƙata a yanzu?”.           Kai tsaye ta amsa da cewar, “Dafin maciji mai matuƙar haɗari”.      “Zako ki sami na macizai ma ba maciji kawai ba. Ki saurari saƙo zuwa safiyar gobe. Mun barki lafiya”.        Wani irin kuka mai taɓa zuciya Iffah ta saki, a hankali ta zame takai kwance kanta da yay mata nauyi na sara mata. Gaba ɗaya duniyar tai mata dummm bata gane komai, burinta kawai shine ta ɓatar da Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed. Gawarsa kawai tafi bukatar gani kwance a ƙasa fiye da komai. So take taga ahalinsa na kuka fiye da wanda sukai a dalilin rasa ƴan uwansu saboda son kansa. Haka ta kwana a wani irin bahagon yanayin da bazata iya koda tunawa ba. Ita bamai barci ba ita ba ido biyu ba, ita ba matacciya ba ita ba mai rai ba gadai tanan. Duk da tana fashin salla ana kiran salla ta miƙe, bayi ta shiga ta tsaftace jikinta duk da babu wani ƙazanta tattare da ita, tana ƙoƙarin naɗe gashinta daya ɗan warware takeji kamar magana a ƙofar ɗakin nata. Cikin shakku ta gyara rigar wankar jikinta ta nufi ƙofa ta buɗe. Da mamaki take kallon amintacciyar hadimarta mai suna Abal dake a durƙushe hanunta ɗauke da ƙyakywan bowl.         Da sauri Abal takai ƙasa tana gaidata. Batare da Iffah ta amsa ba ta ɗaga bakinta da yay mata nauyi da ƙyar tace, “Lafiya.....?”     “Lafiya Lau ya Zawjata-almilk. Saƙone daga sashen mai Babban ɗaki”.       Hakan ya ɗan saka Iffah a shakku da mamaki, amma sai bakinta yay mata nauyi bata iya ta sake cewa komai ba ta amshi tambulan ɗin mai ɗauke da sabuwar madara fara ƙal. Idanu Iffah ta tsurama madarar wani shawa'ar shanta na fusgarta. Amma sai ta dake ta ajiye ta da nufin sai ta gama kimtsawa tasha ko kaɗanne kaffin ta sake komawa barci. Harta nufi kayan data fiddo zata saka kira ya shigo wayarta. Ruɗewa tai dan abune da bai taɓa faruwa da ita ba, kofa sallar asubahi ba ayi ba. Kamar wadda ake ingizawa da remote ta ɗauka wayar, ganin Miran Jasim ta amsa da tsumar jiki tana gaisheshi kai kace yana a gabanta ne. Bai amsata ba, sai ma umarni daya bata cikin kakkausar murya saɓanin wadda yake mata magana da ita a baya.       “Wannan madara ce mai ɗauke da dafin macizai masu haɗarin gaske har guda biyar, daga yanzu zuwa ƙarfe takwas na safiya ina buƙatar jin kukan mutuwa. Kukan mutuwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed nake buƙatar ji har gadon barci na ta dalilinki”.      “An gama ranka ya daɗe”. Iffah ta amsa da rawar murya hawaye na ciko mata ido ga girmamawa har tana rissinawa kamar tana a gabamsa.........✍️       *_🤦ALLAH sarki Iffah baki shike yanka wuya. Kin ɗauka niyya badan zuciyarki zata iya ba a zahiri, gashi masu babban burin sharri zasuyi jifa da hannayenki batare da kin san illar hakan ba a gareki._*       *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_49_* .........Tunda al'amarin nan ya faru babu wanda zai ce yaji koda motsinsa a masarautar hatta hadiman dake zagaye da sashen nasa. Har masu dafa abinci da amintacen hadiminsa dakan iya ganinsa ko kai masa saƙo ma ba ganin nasa suke ba. Abinci kuwa yanda suka shirya haka suke kwashesa. Amma hakan baisa sun gajiya ba kasancewar aikinsu ne. Yau ma kamar kullum sun tsaftato ko'ina sun kuma bajesa da ƙamshi mai taɓa kuzarin mai shaƙa. Bayan an haɗa abincinsa da duk a kwanakin nan yanda ake shiryashi haka suke zuwa su kwashe duk suka koma hawa na uku da shine dai wajen zamansu, sai amintacen hadiminsa da kawai ke da lasisin zama a hawa na karshen ne yay zaman gadin abincin gudun samun matsala duk da babu wani mahaluki a zahiri daya isa ketowa har nan ya saka wani abin cutarwa da ake tsoro.            Kusan ƙarfe takwas abinda hadimin bai zaton gani ko tsammani ba yay matuƙar kidimashi. Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ne da suka kwashe kusan kwanaki takwas batare da sanyashi a idonsu ba ke tunkaro falon cikin takun ƙasaita da izza. Cikin rawar jiki da ruɗani hadimin ya zube a ƙasa bakinsa har rawa yake wajen miƙa gaisuwa. Kamar yanda ya saba kai kawai ya ɗan jinjina batare da damuwa da hadimin ya gani ko bai gani ba ya gittashi ya wuce. Hadimin ya ɗan lumshe ido da zuƙar daddaɗan kamshin shugaban nasa yana mai sauke ajiyar zuciya a ƙasan maƙoshi.      Tajwar Eshaan da baima san yanayi ba a hankali ya kai zaune cikin kujera ya harɗe ƙafafu cikin salon zama irin na sarakan da suka isa. Sai a lokacin hadimin ya zaburo ya sake zubewa gabansa.      “Ya shugabana ko ana bukatar shayi?”.       Kansa kawai ya ɗan jinjina alamar eh yana kauda fuskar sa gefe. Da sauri hadimin da ke satar kallonsa ta gefen ido ya miƙe, haɗaɗɗen daning table ɗin mai cike da kayan breakfast ya nufa, cikin abinda baifi mintuna biyu ba ya dawo ɗauke da ƙaramin tray da butar shayi a samansa. A ɗan tebirin gaban kukerar da yake zaune ya ajiye. Ya tsiyaya shayin a ƙaramin kofin. Baya yaja sosai kansa a ƙasa cikin ƙanƙan da kai yace, “An kammala ya shugabana”.       Baiyi magana ba, bai kuma motsa ba har bayan wasu mintunan biyu. Bayan ya kai shayin bakinsa kusan sau biyu ya ɗan dubi hadimin dake tsaye kai a risine ya sake kauda kai. Maganace a bakinsa, amma sai da ya sake jan wasu sakkani kafin ya furta ta a fisge.      “Mike faruwa a daular ruman?”.   Tambaya mafi rikitarwa, mamaki, al'ajabi harma da ruɗaki ga duk wanda ya jita a bakin da ba'ayi tunani ko tsammani ba ce ta riski hadimin. Falon ya shiga waw-wai-gawa cikin tsumar jiki. Tabbas shine dai akaima tambayar ba wani ba. Sai duk ya sake ruɗewa ba shiri ya zube ƙasa akan guyawunsa. “Kariyar UBANGIJI da ingantacciyar lafiya su kasance ga shugabana, abubuwa da yawa sun faru marasa daɗin faɗi da sauraren ji. Sai dai ban san wanne ake bukatar na isar ba”.         Tamkar ma bashine ya buƙaci jin ba, tsahon wasu mintuna da zasu iya kai huɗu ya sake amsawa ciki-ciki.     “Komai”.   Kai hadimin ya jinjina yana mai sake ƙan-ƙan da kai, ya fara zayyano komai tiryan-tiryan tun daga randa aka ɗauke Iffah sashen har zuwa yau ɗin nan da yake gabansa. Ya kare da faɗin, “Idan na faɗi abinda ba shi shugabana ke buƙatar ji ba ina mai neman afuwa”.         Idan gunki ya motsa bayan ƙare abinda ya buƙaci ji to ya motsa. Hadimin dama dai baya tsammanin samun sharhi ko tambaya ko fashin baƙi daga abinda ya faɗa, dan haka yaja bakinsa yay shiru yana ɗan satar kallonsa ta gefen ido. Ba yau ya fara ganin Tajwar Eshaan ɗin ya danna wani abu a gefen kujerar da yake zama computer ta bayyana ba kamar yanda yayi a yanzu, sai dai a iya hasashensa da dube-dube idan yana gyaran saman ya kasa gano komai......               ★★... KAUYEN JUMNA ★★     Hukuncin da kaka ya yanke, sakamakon tashin hankalin da suka kwana a ciki shi da Ummu da Iyyani tun da sassafe suka fito da nufin komawa gidan Babiy na daular ruman gaba ɗayansu. Kaka ya gama shirya tunkarar kowa gaba-da-gaba a yanzu, dan haka babu ko ɗar tattare da shi. Saurayin nan na kwanaki dake ƙoƙarin shigowa layin gidansu yay saurin taka birki idanunsa a kansu. Tabbatar da su ɗinne dai ke tafe a ƙafa ya sashi ɗaukar wayarsa da sauri-sauri ya latso wata lamba. Sai da tana gab da tsinkewa aka ɗaga, da ƙyar ya iya haɗa haruffan sallama bai jira an amsa masa ba ya ɗora da faɗin, “Oga abin mamaki gasu nan suna fitowa da alama ma garin zasu bari”.        “Woow interesting”.    Aka faɗa daga can cikin nuna ci da birgewa. Sai kuma aka ɗora da faɗin, “Maza ka juya ka koma kan ainahin hanya kafin su isa. Ka tabbatar nan da mintunan da basu wuce hamsin ba na gansu a gabana”.     “An gama boss”. Saurayin ya faɗa da tsantsar girmamawa. Sam su Kaka dake tafiya hankalinsu bai kai kan motarba saboda Ummu dake tafiya a wahale, idan ma ta taka ɗaya biyu sai sun tsaya ta huta kafin su cigaba. Yayi jira na kusan mintuna goma sha ɗaya kafin su iso inda tuni ya iso shi yay fakin. Da sauri ya fito daga lungun daya laɓe hanunsa riƙe da leda yana ɗan cillawa yana ƴar wakarsa. Kamar wani shiri sai ko idon Kaka dake ma Ummu nasiha ta daure su ƙarasa akan wannan saurayi. Yay ɗan jimm alamar shan jinin jiki, sai kuma ganin yanda saurayin ya gittasu babu alamar ya gansa ya sashi zabura.       “Ƴan samari na ce ba...?”    Kamar saurayin bazai kula ba sai kuma ya juyo a ɗan yatsine yana faɗin, “Kace mi....?” sai kuma ya ƙi ƙarasawa da nuna alamar shock kamar gaske. “Ya ALLAHU wa nake gaji haka kamar Baba?”. Kaka ya sauke ajiyar zuciya da jin shakkunsa gaba ɗaya ya gudu yay ɗan murmushi. “Kaga ja'iri ni ne ɗin dai, yaushe haka a gari babu labari?”. Kai a sunkuye saurayin ya shafa ƙeya yana murmushi. “Afuwa kaka uziri ne ya ciyoni har nai ƙudirin shallakeku a karo na biyu batare dana leƙa ba. Yanzu haka ma nan jirana ake saƙo na amsa anan ɗin fatana na kai Dahab (Daular ruman) kafin cikar awa ɗaya da rabi”.        Cikin jin daɗi Kaka yace, “Kai Alhamdullah da wannan zance. Ka ganmu muma can ɗin muka nufa a she da rabon ba sai mun sha wahala ba na jiran mota ma”.      Saurayin ya ɗago irin da mamakin nan, irin sai yanzu ya lura da su iyyanin nan. Gaishesu ya fara da ban haƙurin bai lura da su ba ne wai. Iyyani ta amsa masa da kulawa tana faɗin babu komai.            “Idan hakane Baba ai ku shiga kawai mu wuce, gaisuwar ma a karasata a hanya”.     “Af, e to kaima kayi zance na gaskiya. Amma ai zamu dakushe maka uzrinka”.           “Ai babu komai baba, sahun giwa ya isa take na raƙumi”.      Fuskokinsu ɗauke da murmushi duk suka shiga, Iyyani da Ummu a baya. Kaka ya shiga ta gefensa. Sai da ya tabbatar sun hau hanya ya gyara zaman norse mask ɗin fuskarsa da ƙyau, handkherciff ɗin gefensa ya matsar jikin ac kamar zai goge ya danna ac'n motar ya ƙure. A take ya busa tare abinda ke jikin handkherciff ɗin gasu Iyyani da kaka suka shaƙa har suna sakin ajiyar zukata kusan a jere. Kashewa yay da sauri yana faɗin, “Af kajini da karambani zansa Baba mura”.       Nauyin da kawunansu ya fara musu ya hanasu damar magana duk suka dafe kai kusan a tare, kaka ne ke ƙarfin halin cewa wani abu amma ya kasa, su Ummu kam tuni sunyi luuu jikin kujera alamar barci ya bugar da su. Kakan ma yay luuu a tasa kujerar. Nannauyan numfashi saurayin ya sauke da ɗan juyawa ya dubesu ta mirror. Tabbatar da sun suma yanda yake buƙata ya sashi janye Norse mask ɗin fuskasa da sakin murmushi ya latse wayarsa. Ana ɗagawa bai jira komai ba ya furta, “Done! boss”.       “Proud of you”. Aka bashi amsa a taƙaice da ga can da latse wayar......        (Ta faru ta ƙare🤦😱)    ★★.... ★★.... ★★.....         Tajwar Eshaan da bai sake bi takan hadimin ba kam hankalinsa gaba ɗaya ya tattara ne ga computer ɗin gabansa a yanda yake harɗe. Cikin nutsuwa yake sarrafata a take saƙonnin da yake buƙatar gani suka bayyana kansu. Hannu ya kai ya sake daidaita gilashin idanunsa da ɗan yamutsa fuska ganin dogon text message ɗin daya buɗo... Dai-dai nan takunta da ƙyamshin sassanyan turarenta ya fara rige-rigen isowa hancinsa tun kafin bayyanarta. Wani irin harbawa daya tilastashi ɗaga ƙwayoyin idanunsa kaɗan ta cikin gilashin yay sai ko suka sauka akanta. Sanye take cikin shirinta da baza'a kirasa mai matuƙar ƙawa ba, ba kuma mai ƙasƙantarwa ba. Babu ko ɗigon kwalliya a fuskarta, ƙamshin turarenta ma a yau ƙasa-ƙasa ake iya jinsa. A zahiri zaka ɗauka yanayin da masarautar ke cikine ya sata kasancewa haka, sai dai a haƙiƙanin gaskiya komai a sukurkurce yake gareta. Duk wanda ya san alwashinta akan Tajwar Eshaan zai kalla wannan lokaci ne matsayin na farinciki a gareta domin ta kusanto hanyar cikar nasararta, sai dai zuciyarta danƙare take da wani irin ruɗani da ƙunci. Amma ta kasa dakatar da kanta, komai yana sarrafa kansa tare da ita ne tamkar wadda ake sarrafawa da na'urar remote. Yanda ta ɗanyi turus kamar wadda ta firgita da ganinsa ne ya sashi maida idanun nasa ƙasa cike da basarwa ga screen ɗin computer ɗin kai kace baima san da ko motsinta ba a wajen.        Da ƙyar Iffah ta iya jan numfashi, yayinda bugun da zuciyarta ke faman yi tsananinsa ya ƙara hauhawa. Sai dai mi, bata iya jin zata dakata duk da wani irin rauni da kasala dake cigaba da mamayeta. Tamkar wata hawainiya haka ta cigaba da takowa da sanɗa har inda yake, ta ɗan rissino ta gabansa ta dire tambulan ɗin hannunta a tebirin gaban nasa batare da tayi magana ba.              Amintaccen hadimin nasa da al'amarin ya zame masa kamar wani sabon abu, yay saurin dawowa hayyacinsa cikin rawar harshe ya fara miƙa gaisuwa gareta. Hannu kawai ta iya ɗaga masa a kasalance dai-dai tana kaiwa a kujerar dake gefen Tajwar Eshaan zaune. Dole ya miƙe da sauri ya fice a falon, dan cigaba da zamansa haramunne. Iffah dake jin kamar ta fasa kuka a dai-dai wannan gaɓar ta ɗaga idanunta da girmansu a yau gaba ɗaya ya shanye da ƙyar ta saukesu akan Shahan-shan da yay tamkar bai san da wani mahaluki mai numfashi a falon ba bayan shi.      “Bar... ka da sa.. fi... ya”.      Ta faɗa a rarrabe tamkar mai koyon magana. Da gaske yau ƴan izzar ne a kasan, dan haka bai nuna alamar yaji ba, dan bai ko motsa ba balle ɗauke ido akan abinda ke gabansa har kusan tsahon mintuna biyu kafin ya ɗaga mata hannu da ƙyar ya cigaba da abinda ke gabansa. A ƙalla da a ainahin Iffahr ta take salon nasa zai soke ta, bakuma zata iya haƙuri ba sai ta maida murtani. Amma abin mamaki sai ta miƙe jiki a saɓule ta nufi daning babu jimawa ta dawo da glass cup. Da kallon ƙasan ido ya bita zuciyarsa da jijiyoyin jikinsa na wani irin tsitstsinkewa tamkar suna masa ishara da abinda ke tinkarosa. A karo na farko takai durƙushe gabansa, tare da buɗe tambulan ɗin data shigo da shi mai ɗauke da tatacciyar madara dake gauraye da dafin macizai daban-daban har kala biyar. Jikinta rawa yake, har shi kansa sai da ya lura da hakan ta kallon gefen ido da yake mata. Madarar da bata wuce rabin kofi ba ta miƙa masa tana mai rumtse idanunta wasu hawaye da ƙarfinsu ya zame mata nauyi a ƙirji na gangarowa da gudun tsiya bisa ƙyakykyawar fuskarta.      Cak ya tsaya daga abinda ya keyi, duk da bai juyo gaba ɗayansa yana kallonta ba, hankalinsa kaf ya koma gareta. Kusan a tare zuciyarsa da jininsa ke tsitstsinkewa. Bashi da bukatar shan madara a wannan gaɓar dan a nasa tsarin da rana ko dare kawai yake shan madara. Sauran lokuta shayi ne mafi rinjaye da ruwa. Amma a yanzu duk da bahagon yanayin da yake jin jikinsa, da wanda yaga yarinyar a ciki sai ya kasa nuna bazai sha ba, tamkar shima ana ingizashi da remote ɗinne ya kai tattausan hannunsa saman nata a karo na biyu. Zabura tayi kamar wadda ke son dawowa hayyacinta sai kuma ta koma laƙwas tare da buɗe idanunta da sukai jazur ta sauke a kansa. Kallon cikin ido sukai ma juna na kusan tsahon minti ɗaya cirr batare da ɗaya su ya motsa ba abinda bai taɓa faruwa da su ba. Shi ya fara janye nasa a kasalance tare da hanunsa da ya zaro kofin daga cikin nata...       A yanzun ma firgigit tayi tamkar wadda ta farka a barci harda ɗan zabura ta kai hannu kamar zata riƙo kofin sai dai abin mamaki shi har ya kaisa kan baki...........✍️         (🤦Da zaka iya jina daga tawa duniyar da nace karka sha😭).       *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_* 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲 ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨ (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆) 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻 *_Part 1 End_* *_(50)_*    ........Dire kofin da ke empty a hanun Tajwar Eshaan dai-dai da komawar Iffah daɓas zaune ƙasan lallausan kafet ɗin kamar wadda aka zarema dukkan numfashi. Ta matse jikinta tana mai ƙoƙarin riƙe tsumar da takeyi tare da miƙewa zumut. Ya kafeta da ido lips ɗinsa na ɗan motsawa alamar son cewa wani abu amma jin kai da ƙasaita ya hanashi yin hakan. Sai kawai yay ƙoƙarin janyewa cike da basarwa amma hakan ya gagara. Shi kansa bai san yaya akai ba, bai san tayaya ba kawai ya samu kansa ne da riƙo hannunta. A tare suka rumtse ido bisa mabanbanta dalilai. Karan farko na fara tasirin dafin macizan da suka gama gauraye jininsa ya matsota a hankali garesa. Babu zato Iffah tajita saman jikinsa da ke fitar da wani irin sirrintaccen ƙamshi mai karya zuciya. Numfashinta ne ya fisga da ƙarfi kamar mai cutar Asthma, ta buɗe ido da sauri dan gaba ɗaya hankalinta ya dawo jikinta. Zumbur ta mike jikinta na wani irin kaɗawa ta fara jan ƙafafunta da baya-baya siraran hawaye da batasan na minene ba na rige-rigen sakkowa. Cikin son danne tashin hankalin dake cigaba da gauraye jijiyoyi da tsokar jikinsa ya ɗago idanunsa da launinsu har ya fara canjawa ya zuba mata, gab taci tuntuɓe da centre table, kaifin idanunsa da tasirin su gareta a wannan gaɓar ya sata zubewa gaba ɗayanta akan tebirin...      Wata irin zufa ce ta fara keto masa a dukkan ƙofifin gashinsa, yayinda tun yana iya ganin Iffah a kusa da shi har ta fara masa nisa. (Tabbas a kwai matsala) ya ayyana a zuciyarsa yana mikewa da ƙyar. Da kallo ta bishi zuciyarta na wani irin mahaukacin bugu tamkar zata buntsiro ta bakinta. Ganin ya shige ta miƙe itama cikin sassarfa, harta nufi ƙofa ta dakata, tamkar an janyo idanunta suka sauka kan computer ɗinsa, janyewa tai dan burinta tabar sashen kawai amma sai zuciyarta ta dinga ingizata ga computer ɗin. Bayanta ta ɗan waw-wai-gawa irin dai na rashin gaskiya kafin ta koma da baya ta zauna a kujerar tasa ta dasama rubutun fuskar computer ɗin ido. A karan farko ƙirjinta yay wani irin masifar motsawa. Tsabar kaɗuwa batama san takai hannu ga computer ɗin ba har rawar jikinta na bayyana. Babu tantama saƙon data turama Ajmaal ne na karshe, kaɗan ya rage zuciyar Iffah ta ɓaro waje a wannan gaɓar, babu shiri ta fara sama dukkan saƙonin data tura masa ne babu ko ɗaya daya goge, kowanne kuma babu canji a date ɗin data tura ne. Ai babu shiri ta fito ta shiga settings ɗinsa na WhatsApp. A Profile ɗinsa, dp pic.. ɗinsa, da komai na dai Ajmaal ɗin data sani ne... “Allahumma ajirni fi musibati wa'akhlifni khairin minha”. Iffah ta ambata a karon farko numfashinta na barazanar barin gangar jikinta, computer ɗin tai ƙoƙarin singumowa gaba ɗaya dan maidata cinyarta akai rashin sa'a ta danna abinda bata sani ba kamar ƙiftawar ido suuu ta shige cikin table ɗin. Ƙwaƙwalwarta neman bugawa tayi tsabar rikicewa, ta shiga leƙe-leƙe a wajen sai dai babu abinda ta gane. Babu shiri ta zabura hanyar da Tajwar Eshaan ya bi tana haɗa hanya.....        A ɓangaren Tajwar Eshaan kam da kyar ya iya kai kansa ɗaki, dan jefa kafar kawai yake batare da yasan inda yake takawa ba. A ƙasan lallausan carpet ɗin ɗakin ya zube yana mai jingina jikinsa da yay sharkaf da zufa jikin gado, duk wata addu'ar da tazo bakinsa ambata yake, a haka Iffah data gano ɗakin da ƙyar ta shigo a ɗimauce. Idanunsa dake a lumshe ya buɗe a hankali suka sauka a kanta. Dukkan ƙarfin halinsa da jarumta ya tattaro ya adana tashin hankalin da ke tattare da shi. A ɓangaren ta itama ruɗanin da take ciki ya bada gudunmawa wajen makantar da ita yanayinsa, cikin rawar harshe idanunta dake tsiyayar hawaye a kansa ta durƙushe ɗan nesa da shi.        “Dan ALLAH na roƙeka ka faɗamin wanene kai? Miye alaƙar ka da Ajmaal?!”.      Babu alamar zai tanka mata, sai dai idanunsa dake sake rinewa jajur na tsaye a kanta ƙyam. Tsahon wasu mintuna ya lumshe su da sake buɗe su a kanta yana cije lips ɗinsa. Ya kauda fuskarsa cike da ƙarfin hali, da son saisaita muryarsa, a maimakon ta samu amsar tambayarta sai saɓaninta ya fito da ga garesa.        “Ki canja madarar da kika bani da wadda ke akan dining. Hatta kofin da na sha daga cikinsa karki bari”. Ya ƙare faɗa a wahale cikin cije baki da rumtse idanunsa.      (Iffah ki nutsu karki tonama kanki asiri) zuciyarta ta ayyana mata. Idanunta ta rumtse da karfi tana gyaɗa kai kamar wadda ake faɗamawa a cikin kunne. Sai kuma ta shiga goge hawayen nata da maida kallonta garesa a yanayin son kare kai.      “Ni ba batun madara na tambaye ka ba. Wanene Ajmaal?!!!”. Ta faɗa a matuƙar tsawace.        Birkitattun idanunsa ya rumtse da ƙarfi dan sam baya son hayaniya, balle ma a irin wannan halin da yake ciki a yanzu. Ya buɗesu kanta shima a fusace har sai da kallon cikinsu ya sakata zabura. Shima cikin tsawar da fisgar numfashi ya ce, “Babu abinda zai amfanar da ke a jin amsoshin da kike buƙata a yanzu. Kije kiyi abinda nace!! Kije!!!!”.      Ba ƙaramin firgici Iffah ta shiga da yanayin nasa ba. A zabure kuwa ta miƙe, batama san taya ta nufi ƙofa ba ganin kanta kawai tai a falo, harta nufi ƙofar lifter ta dawo da baya, tambulan ɗin madarar ta ɗauka, ta nufi dining wajen wanke hannu ta juyeta, kofin ta ɗauraye jikinta nata ƙyarma, gaba ɗaya ta nema jarumtarta ta rasa, sai da ta tabbatar ya fita ta dawo kan dining ɗin inda aka shirya break fast, madarar dake a jiye a wani tambulan ta ɗaga ta juye a wanda ta wanke ɗin, ta sake komawa ta wanke wannan, sai kuma ta rasa ina zata ɓoyesa kamar yanda zuciyarta ke bata shawara. Da kyar ta samu nutsuwar samun wajen makalasa, ta dawo harta sake nufar hanyar fita ta sake dawowa da baya, kofin da ya sha madarar ne, shima ɗauka tai ta wanke ta zuba sabuwar madarar ta kauraya ta maida inda ya sha. Sake nufar ƙofa tayi sai kuma ta sake dawowa ta nufi ɗakin dai da ka ganta kasan tana a cikin halin ɗimuwa....     A ɓangaren Tajwar Eshaan kam tana fita tari ya sarkesa, jin saukar abu a tafin hannunsa da yake tare bakin ya sashi saurin kallon hannun. “Jini..” ya ambata a hankali saman lips, sai kuma ya saki wani irin wahalallen murmushi da mai da kansa ya kwantar jikin gadon yana ambaton “Sunci nasara, sun sami nasara ta dalilinki *_My Sohaa_*....” tari ya kuma sarƙesa a hankali, sai dai murmushin na nan maƙale a fuskarsa har yanzu, sai faman lumshe idanunsa da suka birkice yake yana ƙoƙarin buɗesu da ƙyar fuskar Iffah da hawayenta ne tsaye ƙyam a cikinsu. Ba mutuwa yake tsoro ba a yanzu, baya da ƙurar da zai barta a ciki, ya tabbatar itace zata sha wahala, wahala irin wadda ba ita yay mata tanadi ba. Hakanne ya zaburar da shi, yaja jikinsa da ke saki gaba ɗaya da ƙyar zuwa telephone..       Ana ɗagawa ya fara magana cikin son ɓoye yanayin da yake ciki. “Duk wani cctv footage na safiyar yau zuwa yanzu na sashe na ka kwashe sa, amana ko kai na haramta maka ganinsa ka ajiyesa gareni, idan kuma na rasa raina ka damƙashi ga Zawja Fareedah....”           Bai bada damar cewa komai ba ya yanke kiran, da ƙyar ya maida akalar wani zuwa Malikat Bushirat....         *_MALIKAT BUSHIRAT_*    Yanayin tashin hankalin da masarautar ke ciki koma a ace ƙasar baki ɗaya dan yau mutanen da suka fito zanga-zanga akan murabus ɗin Tajwar Eshaan sunfi na kullum yasa ko fita batayi. A kallo ɗaya zaka iya ƙirga damuwarta saman ƙyakykywar fuskarta data koɗe matuƙa a cikin kwanaki ukun nan. Tayi duk wani ƙoƙarin ta iya iyawa domin ganin gudan jininta amma al'amarin ya gagara. Kuka bata san iya adadin da tayi ba ba kuma ta san wanda zatayi a gaba ba, dan anzo gaɓar da ko'a mafarki bata taɓa sakata a lissafin ƙaddararta ba.....       Shigowar kira a landline ɗin ɗakin barcin nata ya sata zabura dan yazo mata ne a bazata, dole ta ambaceshi da bazata dan Tajwar Eshaan ne kawai ke da wannan hurumin. Har tuntuɓe taci amma bata damuba ta caɓi kan wayar tunkan ta karasa gareta da ƙyau. Rawar jikinta dana harshe na faruwa ne a lokaci guda, sai dai muryar data doki tsakkiyar dodon kunnenta ta saka numfashinta tsaiwar wucin gadi....     “Ammie!...”   Aka faɗa da ƙyar cikin kuma rawar harshe mai fidda sautin nakasashshiyar murya mai tabbatar da amon razani ga mai saurare.           “Saiful-malik!!...”     Ta ambata itama tare da fisgar numfashinta dake kaikawo a iya maƙoshinta zuwa cikin baki kawai. Shi bai sauka a huhu ba, bai kuma fita ta hanci ba. Bata ma san ta saki wayar ba ta fice...      “Ya ALLAH Akia!...” Jasrah dake shigowa ta faɗa da sauri tana riƙo Malikat Bushirat da gaba ɗaya idonta ya rufe da ruɗani. Son ƙwacewa take tana ambaton “Eshaan.. Jasrah Eshaan.. Eshaan zasu kashe min shi”.           Sam Jasrah bata fahimci inda ƴar uwar tata ta dosa ba, dan haka tai saurin katseta da faɗin, “Na shiga uku Akia dan ALLAH nutsu kimin bayani, mi ya dakesa?”.       Ina Malikat Bushirat ta kasa amsata, dan numfashinta ma har ya fara fisga. Bata haɗa soyayyar Tajwar Eshaan da komai ba a duniya. Tana masa wani irin makahon so mai wahalar fahimta. Duk yanda Jasrah taso tanƙwarata ta kasa, sunan Eshaan kawai take ambata da son fisgewa ta fita. Bazai yiwu ta barta ta fita a haka ba, dan haka tai saurin danna ƙofar bedroom ɗin da ƙafa. Hankaɗata Malikat Bushirat tayi, duk da taji zafi dama gata ba wani ƙwarin jikin take ji ba amma haka ta daure ta murza key. Da ƙyar ta iya zarewa ta sake riƙo Malikat Bushirat tana mai fashewa da kuka. “Akia dan ALLAH ki sanar min, fitarki a haka ba itace mafita ba, idan ma akan masu zanga-zanga ɗin nan ne ki kwantar da hankalinki jami'an tsaro bazasu barsu su ɓalla koda gate na farko ba........”       “Jasrah ki fahimceni.....!!!” Malikat Bushirat ta katseta cikin ƙaraji sai kuma ta fashe da kuka. Tabbas babu lafiya, ƴar uwarta a haka lallai akwai matsala. Har taune harshe take wajen ambaton, “Zan fahimceki faɗamin ko a taƙaice ne Akia dan ALLAH”.          Da ƙyar Malikat Bushirat ta sanar mata a dunƙule, nan fa hankalin Jasrah ya tashi itama babu shiri ta zabura ta buɗe ƙofar......          ★★....       Suɓucewar kan wayar a hannun Tajwar Eshaan dai-dai da sake faɗowar Iffah ɗakin a birkice. Gaba ɗaya ma ta mance matsayinsa da nata, tai kansa babu alamar hankalinta na tare da gangar jikinta. Tana zubewa gabansa yana faɗowa jikinta hannunsa dafe da kansa yana ambaton “Ammie...” a hankali, ga wata irin zufar da tai masa sharkaf kai kace wanka yay a lokacin.       “Na shiga uku ni Fhareedah!”. Da Iffah ta faɗa cikin kuka ya saka shi ɗago idanunsa dake matukar jazur zattashin hankali. Akanta ya tsaidasu a wani irin bahagon yanayi, ya lumshesu da ƙyar ya sake buɗewa a kanta. Lips ɗinsa da suka koma jajur saɓanin pink a da suna motsa a hankali ya saki wani wahalallen murmushi da har Iffah ta koma ga ALLAH bazata taɓa mantawa ba, dan ya zauna a allon zuciyarta tamkar rubutu akan dutse. kafin idon nasa ya koma ya lumshe gaba ɗaya tattausan hanunsa na dama saƙale cikin nata da bata san sanda ya riƙo ba...........✍️          *_ALHAMDULLAHI!!🙏_*    Ina godiga ga ALLAH daya bani ikon kawo ƙarshen littafin DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA kashi na farƙo. Ina roƙon UBANGIJI ya bani tsahon rai da lafiya ni da ku har zuwa bayan salla da zan ɗora kashi na biyu insha ALLAHU. Ina mai baku haƙuri da ƙari saman haƙuri da tangarɗa da jinkiri da aka samu duk da Alhamdullah ban taɓa fashin posting ba, sai dai labarin yayi tafiyar hawainiya saboda yanayi, hakan ta samune  dalilin babban dalili daya shafi uzirin rayuwata. Insha ALLAHU bayan salla zakuga canji ayi haƙuri amin afuwa dan ALLAH yau da gobe kenan kun san Bilyn taku ba haka takeba a da.🙏🥲.         Himmm!! Ban san ma mizan ce mukuba daga ƙarshe, amma ku sani DAUƊAR GORA part 2 zai zama na musamman ne da salo mai..... (🤭hummm badai sai nace komai ba..) ★Yaya kuke tunanin rayuwar Iffah zata kasance ne?. ★Mizai faru da Tajwar Eshaan zai mutu ne kokuwa?. ★Waye saurayin daya kwamushe su Kaka?. ★Taya Tajwar Eshaan ya zama Ajmaal?. ★Wacece ta ƙurya?. ★Miran Jasim da Miran Arshaan zasu ci nasara?. ★Anya ƴan ƙasar ruman akwai mai iya kwantar da fushinsu a wannan gaɓar?. ★Yaya makomar su Babiy da Barrister?.       Kai tambayoyin da yawa suke karna cikaku da zance Ni ban baku cigaba ba. Kudai kawai muyi addu'ar ALLAH ya kaimu a gama azumi lafiya. Ya rabbi kasa muyi karɓaɓɓiyar ibada. Ina ƙaunarku masoya, zan cigaba da ƙaunarku kuma. Duk wanda ya soni domin ALLAH shima ALLAH ya soshi haka😭🙏😍😍🤩🥰😘. Taku Bilyn Abdull ce😉👍😄.   *LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA* *DAUDAR GORA Billyn abdul* *KI KULANI hafsat xoxo* *A RUBUCE TAKE Huguma* *RUMBUN K'AYA Hafsat rano* *IDON NERA Mamuh ghee* _LITTAFI DAYA: 400_ _LITTAFI BIYU: 600_ _LITTAFI UKU: 800_ _LITTAFI HUDU :1000_ _LITTAFI BIYAR: 1200_ _KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_ _TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_ _TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_ _TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_ _TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_ _ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_ ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN MARYAM SANI ACCESS BANK 0022419171 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 09033181070 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09166221261 *ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA* +227 96 09 67 63 Books biyar 1250CFA Books hudu 1050CFA Books uku 850CFA Books biyu 650CFA Bookk daya 450CFA KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*