[7/15, 1:18 PM] null:       ⚔️*🔥ƘARFE A WUTA🔥*⚔️ MALLAKAR AISHA ADAM (AYSHERCOOL) MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Writer of Gaba da gabanta Ƙanwar maza Cutarwa Ruɗin ƙuruciya Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/9VaPywkyyIhh3g *BISIMILLAHIRAHMANIRAHIM* *Labarin ƙarfe a wuta, ƙirƙirarran labari ne, idan yayi kamanceceniya da rayuwar wani ko wata, arashi ne.* Ban lamunci a juya mini littafi, ta kowace irin siga ba, sai da izinina❗ Page 1 Tsit ƙaton falon yayi, ba ka jin sautin komai, sai ƙarar gudun AC. Sai mutanen falon da suke tsaye sun yi cirko-cirko, kamar masu jiran wani sakamako. Wata matashiyar budurwa ce, durƙushe a kan gwiwoyinta, fuskarta ɗauke da wani yanayi na tsantsar damuwa, da tashin hankali, fuskarta tayi sharkaf da hawaye. "Yanzu sakamakona kenan a wurinki? Irin wannan sakamakon shi na cancanta daga gare ki ko?" Cikin ƙulewa wata babbar mace ta ce "Dama wani sakamako ka ke saka ran samu daga tsintaccaiyar mage? Ai ba za ta taɓa mage ba, abun da na din ga ankarar da kai kenan, tun a shekarun baya, amma ka kasa ankarewa, yanzu ta nuna maka ita ƴar kunama ce" Budurwar ta yakice gumin da yake tsatstsafo mata, ba tare da nadamar abubuwan da suke gudana ba a ƙasan ranta, a zahiri ta ce "Ba mummunan sakamako bane ba, abun da ka tarbiyantar da ni a kai ne, gaskiya ita nake tsaye a kai, bani da niyyar cutar da kowa a gidan nan, kowa aikinsa yake yi, yakamata ayi mini adalci, ba a goyi bayansa a nuna ni ce nake kan ƙarya ba, a bari nima na yi nawa aikin" Cikin tsawa ɗaya matar ta ce "Har wata gaskiya ce da ke..... Dattijon ya ɗaga mata hannu ya ce "Ya isa haka, tashi ki je, ba na ko son ganinki, ki je ki yi abun da ki ke ganin ya dace da ke". Cikin rauni da tashin hankali ta ce "Abba, ba ka son ganina ka ce?" "Eh mana, idan har ki na gudun ɓacin raina da fushina, dole ki ba wa ɗan uwanki duk wani cikakken haɗin kai, domin gudanar da aikinsa yadda yakamata" Cikin matsanancin tashin hankali ta ce "Amma Abba ni kuma menene makomata...? Yakamata a ji ta bakina Abba" Bai tsaya sauraron mai za ta ce ba, yayi gaba zai bar falon. Cikin matsanancin tashin hankali, ta riƙe ƙafarsa ta na fashewa da kuka. "Haba Abbana, me yayi mini saura a duniya, idan har zan rayu ka na fushi da ni, ka yi haƙuri zan yi abun da ka ce in sha Allah" tuni hawaye ya cigaba da wanke mata fuska, tsantsar nadama da damuwa suka mamayeta, ta din ga kuka da sheshsheƙa kamar ta shiɗe, amma ya fizge ƙafarsa ya yi gaba. Yana barin falon, tamkar mutanen falon za su cinyeta ɗanya, haka suka yo kanta sa surutu, kowa da abun da yake faɗa. Tashi ta yi tsaye, ta goge hawayenta, cikin ko in kula, ita ma ta bi wata hanyar ta bar musu falon, cikin sigar kwa ci kanku. Ɗakinta, ta shiga ta buɗe drower, ta fito da wasu takardu ta zube su a kan gado, ta kunna system ɗin ta da take caji a gefen gadon, lokaci guda kuma ta ɗauki wayarta tana dannawa. Jin motsin mutum a bayanta, ya sanya ta waiwaya da sauri. A tsaye ta ganshi bakin ƙofa, fuskarsa babu walwala balle annuri. Mayar da hankali ta yi, za ta cigaba da danna wayarta, ya tako zuwa gabanta, ya tsaya ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Kin shirya aikata abun da aka umarce ki ko kuwa?" Cikin hanzari ta tari numfashin sa ta ce "Ban ce shirya ba, kuma ba zan shirya ba, daga nan har gaban abada, ka fita ka rabu da ni". Cikin matuƙar mamaki yake bin ta da kallo, "Yanzu duk kukan da ki ka yi, ƙarya ki ke yi kenan?" A hasale ta ce "Ina ruwanka, idan ma kukan ƙarya ne ko na gaske, ka yi aikinka in yi nawa, kar ka sake yinƙurin shigar mini aiki, idan ba haka ba komai yana iya faruwa, wallahi ba zan fasa abun da na yi niyya ba, idan kuma ka cigaba da takura mini, zan baka mamaki" Hannu ya saka, ya ɗagota daga kan gadon ya ce "Menene zai faru, wani irin mamaki zaki bani? Me zai faru nake son ki gaya mini. Kina da hankali kuwa? Kin san doka amma kina taka ta yadda ki ke so? Da me ki ke taƙama ne haka?" "Doka ko? Ni  iya takata na yi, kai kuma cin zarafinta ka ke ƙoƙarin yi, ka ƙyale ni babu ruwanka da ni, ka yi naka aikin na yi nawa duk wanda yayi galaba shikenan. Idan ka ga dama ka je ka sake gayawa Abba abun da duk yayi maka a kaina, wallahi babu gudu babu ja da baya, ban fara dan ina saka ran dainawa ba, ba tare da na yi nasara ba" hankaɗata yayi kan gadon, yana wani irin huci, zuciyarsa na yi masa zafi, yayi wata irin ƙwafa yana bin ta da kallo. Cikin hanzari ya fice ya bar mata ɗakin, saboda idan ya cigaba da tsayuwa, zai iya yi mata abun da ba shikenan ba. Ta yinƙura ta tashi zaune tana haki, tana kallon ƙofar da ya fita. **** Tsaye take a gefen wani gini, tana ƙarewa harabar kotun ido. Yadda aka cika harabar da manya da ƙananan motoci ne, ya sake tabattar mata da manyan shari'oi za a gudanar a yau. Ta din ga kallon agogon hannunta, tana kallon gate shigowa harabar kotun. Motar gidan yari ce ta shigo, aka yi parking ɗin ta, sai dai tsayuwar motar babu daɗewa wata danƙareriyar motar, ta shigo harabar kotun. A ƙalla an kai mintuna goma da parking ɗin motar, sannan aka buɗe bayan motar, wata mata ta fito, sanye cikin coat. Mutanen da ke harabar wurin, suka nufeta, wasu suka karɓi jakarta, ana ta yi mata fadanci, cikin girmamawa. "Ya Allah kai ne Allah, kai ne buwayi gagara misali, Ubangiji da babu wani kafinsa, kuma babu wani a bayansa. Allah na san mutanen nan sun fi ƙarfina ta ko ina, amma kaine abun dogaro na, na san ba za ka bani kunya ba. Allah sun fi ƙarfina ka fi mini ƙarfinsu. Allah ka yi mini kunfayakununka a kan shari'ar nan, hasken gaskiya ya shafe duhun ƙarya, duk da ina da masu goya mini baya, amma Allah goyon bayanka nake buƙata" ta jima a tsaye tana karanto addu'a, tare da yi wa Allah kirari. A hankali ta furta "What a hectic trial, Ubangiji ka iya mini" cikin nutsuwa, ta fara taka takalminta mai tudu, ta nufi shiga cikin kotun, da takunta mai kama da na ƙasaita, shigarta ta lawyoyi tayi matuƙar yi mata kyau, tana tunkarar ƙofar shiga, zuciyarta na tsananta bugawa,tana fatan Allah ya shiga lamarin ta. **** Ƙofar famfo kano state. Ƙarfe goma saura mintuna goma na dare, tuƙi yake yi cikin sauri, saboda yadda fasinjar da ya ɗaukko take azalzalar sa. Duk saurin da yake yi, mita take yi masa, a kan ya ƙara gudu. Yanayin kwalliyar da ta yi, cikin baƙin material, fuskarta ta sha make-up, zai  tabattar maka daga wurin biki take. Ta kalli agogon hannunta, kamar ta fashe da kuka ta ce "Mai napep, ka yi wa girman Allah ka yi sauri" Ya ce "Wai dan Allah hajiya yaya ki ke so na yi ne? Haba babata duk saurin da nake yi, ki yi haƙuri mana mu tafi a sannu". A ƙule ta ce "Ban gane babarka ba, wani irin wulaƙanci ne wata babarka, na yi maka kama da tsohuwa ne?" Yayi murmushi ya ce "A'a, ai ku mata duk in da ku ke iyaye ne... Katse shi ta yi ta hanyar cewa "kuma sai aka ce na haifi kamar ka? Ai sai a bari na haifa tukuna, a yanzu na haifi kamar ka, ai tawa ta ƙare a duniya. Ko yayarka ka ce mini ka cuce ni, balle babarka. Ni dai ka ƙara sauri, yau na san kashina ya bushe, sai an yagalgalani da masifa a gida yau. Aikin banza, ƙawayen amarya ƴan wahala, mun gama wannan wahalar a ɗauke ta a mota an kai ta gidanta, mu muna fama a titi. Mu ma Allah ya kawo lokaci, ace ga miji ga mota" Ya waiwaya ya kalleta yana murmushi, a fusace ta ce "Lafiya malam?" "A'a Allah ya baki haƙuri". Kafin su ƙarasa in da zata sauka, ta ciro masa kuɗinsa, su na zuwa in da za ta sauka, ta miƙa masa, ta sauka tayi cikin layinsu da gudu a kan takalminta mai shegen tsini, ko wahalar gudun ba ta ji. Mayafinta da jakarta a hannu, ta tura gate ɗin ta shiga ta na haki. Wani matashin saurayi, yana tsaye a harabar gidan hannunsa riƙe da waya, ya kalleta ya ce "Daga ina ki ke?" "Biki" ta bashi amsa kai tsaye. "Za ki ci ubanki kuwa, Major yana nan ido biyu, tun ƙarfe takwas ya dawo yake tambaya ko kin dawo, gashi kin kashe waya ke ga ƙwararriya" Cikin ta yayi wata ƙara saboda tsoro "Allahumma inni as'aluka afuwa wal afiya, yau na kaɗe" ta ƙarasa maganar tana nufar cikin gidan. Cikin sanɗa ta shiga falon, sai dai tana shiga, ta fara tozali da dattijon zaune a kan kujera 3 seater, ya sanya ƙofar shigowa falon a gaba, da gani babu tambaya ta san ita yake jira. Tsayawa tayi ƙyam da takalmanta a hannu, da jaka da mayafi, kamar ta juya da gudu ta koma. "Daga ina?" Yayi mata magana cikin dakakkiyar muryarsa. Cikin rawar murya ta ce "Abba, wurin biki" "To juya ki koma in da ki ka fito" "Ai an tashi" tayi maganar kamar ta fasa ihu, dan tuhumar Abba babu daɗi. "Dama haka mu ka yi da ke? Ki fita ki je ki yi zamanki? Ki dawo mini gida bayan goma, sai ka ce ki na zaman kanki?, koma ki kwana a in da aka yi bikin" "Dan Allah Abb.." "Get out, kar ki kuskura ki yi mini magiya. Duk gidan nan babu mai bani ciwon kan da ki ke bani Arfa, koma in da ki ka fito ba ki da wurin kwana a cikin gidan nan yau" da gudu ta juya ta fita saboda tsorata da ta yi. Ta koma harabar gidan, a ƙasan zuciyarta ta ce "Na shiga uku, ni ake kora kamar wata karya, yanzu idan gidan mijina ne, ba sai dai ya gama bala'in in shige ɗaki na bar shi ba.. Ba ta gama tsinkewa da lamarin ba, sai da major ya kulle babbar ƙofar shiga cikin gidan. Ta zube kayanta, ta tafi famfon harabar gidan, ta dinga wanke fuskarta, ta wanke kwalliyar fuskar gaba ɗaya, ta koma ta zauna jiran tsammani ko Allah zai saka Abba ya buɗe mata ƙofa. Samarin gidan suka fara fitowa daga BQ, suna shimfiɗa a harabar gidan, za su yi kwanciyar zafi. Sai wulaƙanci suke yi mata, suna yi mata Allah ya ƙara, suna kyararta, kamar wadda ta aikata wani gagarumin abun kunya. Ganin ba ta da mafita, ta laluba ta samo tabarma ta shimfiɗa, ta yi kwanciyarta dan a gajiye take sosai. Tsakar dare, ta yi juyi, ta ji babu kowa a kan gadon sai ita kaɗai, mamaki ya kamata, ta kalli agogon wayarta, biyu da rabi na dare. Tasowa ta yi ta fito nemansa, sai dai ga mamakinta, ta tarar da shi a ventilation ɗin saman bene, ya zauna a kan kujera ya saka harabar gidan a gaba, hannunsa riƙe da ɗan ƙaramin Alqur'ani yana karantawa. "Lafiya dai?" Tayi maganar cikin mamaki. Ya waiwaya ya kalleta ya ce "Lafiya ƙalau" "Amma me ka ke yi a wurin nan, a wannan uban daren? Na zata tuni ka kwanta, na fito na duba falo baka nan" Cikin ko in kula ya ce "Kar ki damu, ki je ki yi kwanciyar ki, Arfat ke  punishment" Cikin takaici matar ta ce "To ta na punishment, sai kuma kai ka zo nan ka zauna, ka hana idonka bacci?" Yayi murmushi ya ce "Ko na kwanta ba zan iya rintsawa ba, ki yi kwanciyar ki kawai" tamkar ta yi tsaki, haka ta wuce shi ta ƙyale shi, tama tunanin yaushe ƙarshen wannan lamarin zai zo?. Haka ya kwana a zaune, yana gadin harabar gidan, duk wanda yayi juyi cikin mazan nan, yana kallon shi. Yana ganin yadda Arfa ke ta juyi, sauro ya dame ta, sai da ya ji tamkar ya sauka ya samu abu ya rufe ta, amma ya ƙyale ta. Asubar fari, ya yi alwala, ya sauka ƙasa domin tafiya masallaci. Samarin na jin takunsa, suka din ga tashi, idan ba haka ba, ya tashi mutum da carbi. Ya na zuwa in da take kwance tana bacci, ya tsula mata carbi a ƙafafuwanta. A razane ta tashi tana rarraba ido. Bai ce mata uffan ba, ya yi gaba ya fice. Tana ganin ya fita, ta tattara komatsanta, ta shiga cikin gidan, sai soshe-soshe take yi, saboda uban sauron da ya cije ta. Cikin ɗakinta ta shiga, ta watsar da jakarta da sauran kayan a kan gadonta, ta jona wayarta a caji. Ta tuɓe kayanta daga ita sai underwear. Wata matashiyar budurwa da aƙalla za ta ɗan girmewa Arfa ta fito daga banɗaki, ta kalle ta, ta ce "Arfa, ke kuwa a ina ki ka kwana? Har sha ɗayan dare ba ki dawo ba" banza tayi mata, ta taho fuuu ta kusa bangajeta, ta shiga banɗaki. Ta girgiza kai kawai ta shimfiɗa sallaya. Da ƙyar ta yi sallar asuba, sai soshe-soshe take yi, tana idarwa ta ɓingire ta hau bacci a wurin. Sosai take baccinta, dan ta gaji sosai, ga baccin jiya sam bai yi mata daɗi ba. "Nabila!Nabila!!" Tsaki tayi tare da jan "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, menene, wannan wane irin kira ne dan Allah?" "Abba ne ya ce, ace miki yana fatan kin ajiye aiki ne, da ki ka kwanta kina bacci haryanzu ba ki fita ba"da sauri ta buɗe idonta, gaba ɗaya ta manta yau Monday. Kamar korarriya ta tashi, ta afka banɗaki, a gurguje ta wanke bakinta, tayi wanka, ta fito ta shafa mayuka, da turaruka ta shirya cikin uniform. Ta saɓa coat ɗin ta a kafaɗa, ta ɗauki jakarta ta goyo, ta sanya takalminta, tayi waje tana kunna wayarta. Ta shiga kitchen, ta buɗe fridge ta ɗebi lemuka ta zuba a jakartab, da abun da ta ajiye da wanda ba ta ajiye ba, duk ta kwasa ta zuba, ta zuge jakar ta fito falo. A falon suka yi karo da wata matashiyar mata, matar ta kalli Nabila ta ce "Ma'aikaciya ko mahaukaciya, kalleki kamar korarriya Nabila, zaki fita aiki amma ki ka kwanta ki na kwasar bacci abinki". Nabila ta ce "Anty, the whole barrister ki ke cewa mahaukaciya?" "Yo banda shirme, kalleki kamar an hankaɗoki, ke wannan wane nutsatstsen ne ma zai ce ki tsaya masa shari'a?" Nabila ta ce "I will fill a lawsuit against you, what you did is deformation of character, the whole barrister Anty ki ka zaga" "Wuce ki tafi kafin na make ki ni? Idan suka kore ki daga wurin aikin, ai kya nutsu" Nabila ta sake kwasa da gudu a kan takalmanta kamar ba budurwa ba. Mai aikinsu ta tarar a famfon harabar gidan, tana wanke-wanke. "Shalelen Abbanta, yau kamar kin makara" Ɗaga mata hannu kawai Nabila ta yi, kowa ya ganta sai yayi magana, ta kalli hanyar benen Abba, kamar ta je ta gaishe shi, amma ta fasa ta san yadda ta makaran nan, sai ya zaunar da ita yayi mata faɗa, ga laifin jiya ga na yau, kuma ta san sai ya haɗa har da na waccan shekarar yayi mata, dan haka tayi wuf ta fice waje. Duk irin vibration ɗin da wayarta take yi, ba ta ɗaga ba sai da ta zauna a cikin adaidaita sahu, sannan ta ɗaga kai wayar kunnenta. "Wai Nabila wani irin wulaƙanci ne, nake ta kiranki ki ka ƙi ɗagawa?" Nabila ta ce "Ke ban son tijara, kin wuce aiki ne?" A fusace mai maganar ta ce "Ban sani ba" Nabila ta yi dariya ta ce "Sorry masoyiyya, ki fito titi gani nan" tafiyar mintuna sha biyar suka yi, suka iske wata matashiyar budurwar a titi, sanye cikin doguwar rigar abaya, ta kama adaidaita sahun ta shiga tana hararar Nabila. "Sorry sumy, kar ki fashe dan Allah" "Wallahi kin fusata ni Nabila" "Shiyasa na ce ki yi haƙuri ai, ya gidan ya su mama?" Sumayya ta ce "Suna lafiya ƙalau, meyasamu fuskarki? Na ga kamar ƙuraje" Nabila ta rausayar da kai ta ce "Ke bari, the whole me, jiya Abba ya saka na kwana a haraba, sauron nan na cikin flowers suka yi idi a kaina" Sumayya ta waro ido ta ce "Wai da gaske?" "Zan yi miki ƙarya ne? Wallahi dattijon nan ya ce wai na koma in da na fito ya rufe ƙofa. Aikuwa na din ga tsinewa amaryar nan, na baro ta a gidanta cikin nishaɗi da farinciki, ni kuma na afka tashin hankali, kamar ni degree holder, Abba ya rufewa gida. Yanzu dan Allah da a gidan mijina ne, da ba sai dai yayi masifar ya gama ba, babu wanda ya ji ya gani? Ai Abba ya tozarta ni jiya. Sai so ake a ga fuska a tuhume ni, ko ayi mini rashin mutunci a gidan nan, kin san gidanmu Allah ya wadata mu da munafukai, ni kuwa na haɗe rai" Sumayya ta ce "Allah ya ƙara, ke uwar gwaninta, har da kai amarya, banda uban anko da ki ka yi mata. Ina mai tabattar miki ke da ganinta ta tako gidanku, sai wani ikon Allah" Nabila ta ɗan yi shiru ta ce "Ku ma fa haka ne, kin san wani abu, ba hassada nake yi wa amira ta yi aure ba, amma kalli na fita kyau fa, na fita komai amma amira ta shige daga ciki, ohh ni Nabila, duk kyan nan da dirin nan yadda ki ka san na je na haye kan high table ɗin nan ayi da ni ranar dinner. Ba ma wannan ba duk wannan gayun da kwalliyar ban yi saurayi a bikin nan ba" Sumayya ta ce "Ki je ki ɗorawa ranki jarabar son aure, ki ƙi focusing a kan career ki, ni ko a jikina na san lokaci ne, kuma tun da ba yawon iskanci nake ba, duk wadda ta yi mini gorin aure sai na ci ubanta, shekarun namu nawa ne duka da za a addaba mana" Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Ba haka ba ne Sumayya, we have a different backgrounds, ke kin san me nake nufi, wallahi ƴanci nake so Sumayya, ko ta halin ƙaƙa" Sumayya ta ce "Kar neman ƴanci ya kai ki ga halaka, duk ina samarin naki ne to?ba wanda zaki tsayar?" Nabila ta yi tsaki ta ce "Bar matsiyata, daga ƴan wahala sai ƴan iska. Sai dai duk wanda ya zo hannuna sai na ci rabona ayi baran-baran. Na daina wahalar son mutum, daga ƙarshe yayi breaking heart ɗina, ya ci bulus. And also haryanzu ban samu spec ɗi na ba kin dai gane" Sumayya ta ce "Au ke yanzu har wane zaɓe-zaɓe ki ke yi?" Nabila ta ce "To ana raba mai rai da motsi ne? Iya wuya akwai abun da zuciya take so, kuma ni na fi son namiji mai kumari sosai. Irin wanda zaki ganshi ingarman namiji mai cikar zati. Beside fuskar namiji ba gemu, ai sunansa sumayya, ni kuma daga dattijai, sai marasa gemu, sai kuma ƴan wahala, ni matashi nake so, ba kuma yaro ba" Sumayya ta ce "Au sunana ne ma abun kwatancen iya shegenki ko, to ki je dan kanki. Mai napep zan sauka a nan, za ta baka kuɗin" Nabila ta ce "Ke uban waye ya ce miki ina da kuɗi?" Tuni Sumayya ta sauka, ta bar Nabila. Nabila ta yi ƙwafa ta ce "Zamu haɗu ne, zaki ga wulaƙanci". *** A hankali yake buɗe jajayen idanunsa, a lokaci guda kuma yana lumshe su, tamkar mai shirin yin bacci. Sai mirgina kansa yake yi, yana sake lumshe manyan idanunsa da suka koma jajaye matuƙa. Tamkar an jefo shi, haka ya faɗo ɗakin, yana rarraba ido. A hankali ya ɗaga kai ya kalli wanda ya shigo ɗin, ya mayar da kansa ƙasa ya sunkuyar. "Allah ya taimaki oga..." Bai amsa ba kawai ya buɗe tafin hannunsa ya miƙa masa. Wata baƙar leda ya ciro, ya ɗora masa a hannun, sannan ya ce "Sai dai Oga ba a samu da yawa ba, ƴar kaɗan ce, cinnaku sun yi wa kasuwar ƙawanya, shiga da fitar kaya na bayar da wahala, da ƙyar na samu wannan wurin wani ɗan inyamura, ina ga wuri zan canza, saboda kamar ana son yi mini cune". Bai ce masa uffan ba, ya kwance ledar, ya fito da kwalin wata allura pack guda, mai ɗauke da ampoule na allura guda goma. Sirinji lamba biyar ya ɗauka, ya din ga fasa alluran yana zuƙa, sai da ya cika sirinjin, sannan ya miƙe hannunsa. Ya ɗaga kansa ya kalli matashin da ya kawo masa allurar, bai ce masa komai ba, matashin ya bar ɗakin. Ya mayar da idonsa kan hannunsa, ya yana kallon jijiyoyin da suka kwanta ɗoɗar a ƙarƙashin fatarsa, suka yi ruɗu-ruɗu, manya da ƙanana. Ya dubi guda ɗaya, ya huda ta da sirinjin hannunsa, ya fara bawa kansa allurar sannu a hankali. Sai da ya zuba ta duka, sannan ya yi jifa da sirinjin, ya sunkuyar da kansa ya na jiran Sakamakon hukuncin da ya ɗauka. Sai dai kusan mintuna goma sha biyar, bai ji abun da yake so ba, sai wani irin nauyi da kansa ya ƙara, idonsa ya din ga yi masa yaji, ya rintse idanunsa amma bai ji alamar abun da yake so ba. Abu kamar wasa kansa ya din ga wani irin sarawa, ƙirjinsa yana zafi. Ya dafe kansa da hannunsa bibbiyu yana jujjuyawa tare da rufe idanunsa. Ihu ya fara yi iya ƙarfin sa yana taƙarƙrewa, yana girgiza kansa, saboda yadda yake jin kansa tamkar zai yi bindiga. Da gudu suka shiga ɗakin, suka fara ƙoƙarin danne shi, amma ya yi ihu ya watsar da su baki ɗaya ya cigaba da kururuwa. Ayshercool. 08081012143 [7/16, 1:53 PM] null:           ⚔️*ƘARFE A WUTA*⚔️ MALLAKAR AISHA ADAM (AYSHERCOOL) MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION *BRIGHT PENS SECOND BATCH* https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g Arewabooks ayshercool7724 Watpad ayshercool7724 2 A ƙalla sun kai ƙarti uku majiya ƙarfi, suka riƙe shi, amma sai ƙoƙarin watsar da su yake yi, ga wani irin gurnani yana yi, kamar mahaukacin zaki. Da ƙyar suka haɗu suka kai shi ƙasa, suka daddane shi yana cigaba da ƙoƙarin watsar da su ya tashi. Ɗaya daga cikinsu da yanayin kamanninsa ya bayyana, ƙarara shaye-shaye ya huda shi, saboda yadda laɓɓansa suke baƙi ƙirin, ga wani irin ƙaton tabo a gefen fuskarsa. A hankali yake ɗan dukan bayansa cikin sigar rarrashi yana faɗin "Easy maza, easy, mun san ka na cikin damuwa da raɗaɗi, amma hakan ba mafita bane ba, ka yi haƙuri muna tare da kai ɗari bisa ɗari iya wuya" ya cigaba da maganar yana rarrashin sa. A hankali jikinsa ya saki, ya daina gurnanin da yake yi, ya lumshe idanunsa, ya rufe su, tamkar mai bacci. Sai da suka tabattar ya yi relaxing, sannan suka ɗaga shi. Major ne tsaye a gaban mudubi, yana ƙara kintsa jikinsa kamar wani matashi, ba dattijo ba, uwargidan sa na gefensa tana taimaka masa yana shiryawa, Ba tare da ya kalle ta ba ya ce "Arfa kuwa ta tafi aikin?". Ta yamutsa fuska ta ce "Ta ga dama ta tafi" Ya jinjina kai ya ce "Punishment ɗin da na yi mata jiya, shi ya hana ta zo ta gaishe ni yau kenan,'? zan gamu da ita ne idan ta dawo". "Dan girman Allah major ka ƙyale sabgar yarinyar nan, sai ka ce itakaɗai ce ƴa a gidan nan, komai ita su duk sauran ba ƴaƴa bane ba, da ba ka damu da lamarinsu ba?" Kallon da yayi mata ne ya sanya ta yin shiru, tare da sunkuyar da kai, bai sake ce mata komai ba, ya ɗauki mukullin motarsa ya fice. Cike da takaici ta sauka daga benen, ta fito main falon gidan tana mita. "Yaya ya dai? Meyafaru ne?" Duk da ba ta kasance mai sakarwa abokan zamanta fuska ba, amma haka kurum ta tsinci kanta da gaya mata abun da ya faru saboda takaici. "Major ne mana, gaba ɗaya ya tattara hankalinsa a kan yarinyar nan, kamar itakaɗai ce ƴa a cikin gidan nan, jiya kwana na ne, amma a barandarsa ya ƙare kwanan jiya, wai yana gadinta, abubuwan nan sun fara isata" Ɗayar ta taɓe baki ta ce "Ai ni na gaji, na zuba ido su ƙarata, abun da ba jiya aka fara ba, ba yau ba". Anty, wadda take ta uku, da take karyawa, duk da ba da ita suke ba ta ce "Amma dai an yi abun kunya, kishi zan ce ko baƙin ciki da ƴar cikinku" A fusace Uwargidan major, da ake cewa Mama ta ce "Asiya, da ni ki ke ko wa?" Anty ta ce "Duk wanda ya tsargu, sai menene dan ya nuna mata kulawa ta musamman, duk kulawar da yake bawa sauran yaran bai isa ba? Ƴaƴa nawa ne a gidan nan, kowanne ya na bashi kulawa dai-dai da buƙatarsa ne, amma da yake kishi ya zame muku bala'i, mussaman ma ke, da kowa ma yi ki ke, kin fi mu daɗewa da shi, amma haryanzu ba ki san halinsa ba" Mama ta ce "Ba zan yi musayar yawu da ke ba ƙanwar bayana, dan ba ki isa ba, da wanda ya ajiye ki zan yi". Anty ta ce "Idan ma ƴar cikinki ce, matsayinmu ɗaya matan major, kuma ni gaskiya nake faɗa" haka suka cigaba da ƴan faɗace-faɗacen su na kishi. Nabila kuwa da wasu lokutan a kan yi mata laƙabi da Arfat, tana zaune a katafaren office, itakaɗai sai aikin danna waya take yi, cikin nishaɗi kamar babu wani abu da yake damunta. Knocking ɗin ƙofar office ɗin aka yi, ta bayar da izinin a shigo. Nabila suka gaisa da matar ta ce "Nabila ko?" Nabila ta jinjina kai ta ce "Eh" "Ki zo Barrister yana kiranki" "Wane barrister?" Matar ta ce "Director. Dama ina son in yi miki magana. Kin ga wurin nan babbar organization ce, da muke dealing da mutane daban-daban, especially manyan mutane. Yana da kyau ki jajirce director baya son ragwanci ko harkar ko in kula da aiki, sai ku samu saɓani" Nabila ta yi murmushi ta ce "Na gane, na kuma fahimta na gode sosai" matar ta jinjina kai ta fita. Nabila ma tashi ta yi, ta fita ta tafi office ɗin da ake nemanta. Ta tarar da shi da wani babban mutum a zaune a office ɗin sa, ta gaishe su cikin girmamawa sannan ta kalli Director ta ce "Sir gani" Ya kashingiɗa ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Nabila, what is actually wrong with you ne?" Cikin mamaki ta ce "Ni kuma? Me na yi sir?" Ya gyara zamansa ya ce "Anya ke ki ke son zama lawyer ko choice ɗin major ne? Tun da ki ka zo wurin nan you don't care, sai dai ki zauna ki danna waya, ki yi ciye-ciye, sai kwalliya. Bama kya shiga cikin ma'aikatan ki ga yadda ake aiki, balle mu ga gogewarki, mu faa tura ki trials, dama zuba miki ido na yi amma na ga baki san zuru ba" Nabila ta yi shiru ta sunkuyar da kanta ƙasa. "Ina buƙatar ganin canji a tare da ke, idan ba haka ba na fara kai ƙarar ki wurin Major, yanzu muna da client da yake son yin apeal, a kan wata shari'a da wasu mutane suka kai ƙararsa. Ki je na saka ki a team ɗin su barrister Habib, ki je ku tattauna yadda za ayi handling case ɗin. Effort ɗinki shi zai sanya na baki manyan cases to help your career" Ta risunar da kai ta ce "Ok sir" ta juya ta fara tafiya, sai dai mutumin da tarar a office ɗin, ya bi bayanta da kallo yadda ƙugunta ke juyawa, cikin skirt ɗin kayan jikinta. Office ɗin Barrister Habib ta je, aka sanar da ita suna ɗakin sirri, dan haka kai tsaye can ta wuce. Ta tura ƙofar ta yi sallama, suka amsa mata, ta nemi wuri ta zauna. Barrister Habib ya ce "Kin ga damar zuwa kenan?" Wani irin kallo ta yi masa, amma ba ta ce komai ba, su kuma suka cigaba da abun da suke yi. Shari'a ce a kan wani attajirin mutumin ya karɓe gonakin wasu ƴan ƙauye, ya basu diyya ya fara ginin kamfanin sarrafa shinkafa, sai dai suka yi ƙararsa diyyar da ya biya su, ta saɓawa yarjejeniyar da suka yi da shi, dan sam bai kai darajar gonakinsu ba. Ganin ba su da galihu, ya sanya bai damu da ƙarar da suka kai shi ba, sai da aka yanke hukuncin ya biya su, sannan ya ce zai yi apeal. Mamaki ya cika Nabila, irin maƙudan kuɗin da ya biya law firm ɗin su, a bashi lawyoyi su kare shi, ya isa ya ƙarawa mutanen nan, ya biya su haƙƙoƙin su. Nabila dai ta yi zuru da ido, tana kallon yadda ake harhaɗa hujjoji na halal da na haram, domin mutumin yayi nasara a kotu. Baƙin ciki da takaici suka isheta, sunan ƙauyen da abun ya faru kawai ya isa ka gane cewar masu ƙaramin ƙarfi ne. Dan galibi mutanen karaka da Allah suka dogara, da harkar noma suka dogara. Tashi ta yi tsaye ta ce "Excuse me please, na fara jin yunwa lokacin cin abincina yayi" Duka lawyoyin da shi kansa client ɗin suka ɗago suka kalleta. Habib ya ce "Ana tsaka da aikin?" Ta basar ta ce"Am sorry, am having a chronic ulcer, za a iya samun matsala, idan na cigaba da zama" daga haka ta ɗauki jakarta ta fice, tana mitar ba zata zauna a ƙulla wannan sharrin da ita ba, ranar lahira ta shiga uku. Ta koma office ɗin ta, ta yi alwala tayi sallar azahar, ta je ta samu Director ta sanar masa da tana da uzuri ta na son ta tafi, yayi mata iznin hakan. A hanya ta tsayar da mai napep, suka ɗauki sumayya, sannan suka tafi. Ta kalli Sumayya ta ce "Sumy, meyafaru ne? Na ga kina wani ɓata rai" Sumayya ta yi tsaki ta ce "Haushin kaina nake ji, da na karanci aikin jarida Arfa" Cikin mamaki ta ce "Amma meyasa, na ga shi ne zaɓinki?" "Wallahi duk ya fita daga kaina, hira aka yi da honorable Indabo, wai an yi borehole a ƙananan Hukumomin da yake wakilta, an raba kayan makaranta ga ɗalibai. An kai bencina makarantun firamare da na islamiyyu. Last week aka ce na je na tattauna da al'umman local government ɗin, na je ni ban ga ayyukan da aka yi ba, na tattauna da mutanen ƙananan hukumomin, sun ce ba ayi musu ba. Na kai recording ɗin, aka saka, wai lawisa ba ta tantance shirin ba, ba ta sani ba aka saka, kin ga cin mutuncin da aka yi mini, wai zan lalata musu business wai sai na je na samo mutanen da zan yi hira da su, su ce eh an yi ayyukan su yi godiya alhalin ba ayi ba. Na zama maƙaryaciya kenan me zan ce wa Allah? Wai har da idan ban yi wasa ba, sai honorable ya saka an ɗaure ni" Nabila ta ce "Ikon Allah, ashe duk kanwar ja ce sumy, yo nima hakan take ai, wani tasonon Alhaji ne ya zo yayi kirim a kan kujera kamar damin doya, ya biya uban kuɗi wai za a kare shi, ya cuci talakawa ko kunya bai ji ba, kuma director ya sakani a team ɗin lauyoyin, ni dai ba zan yi ba wallahi, sai dai ya yi ta gaya wa Abban. Haka kurum a cuci mutane ka je ka cewa Allah me?" "Wallahi Nabila, ba ki ji zuciyata ba, yanzu sai dai na je na tara maƙwabta na yi hirar ƙarya da su, a zo a sake sakawa, kuma wai sai na rubuta takardar ban haƙuri, ki ji fa" Nabila ta ce "Tirƙashi, wai ya ɗaure ki, to ya ɗaure ki shi ma ya hau da ɗaurin Allah " Haka suka cigaba da tattaunawa, har suka isa in da sumayya za ta sauka. *** Cikin tsananin tashin hankali, yake magana, kallo ɗaya zaka yi masa ka san hankalinsa a matuƙar tashe yake. Ya daki teburi ya ce "Kwamishina, dole fa ku nemo yaron nan, dole ku mayar da hankali a nemo shi a duk in da yake a ƙasar nan" Mutumin da yake zaune cikin kakin ƴan sanda ya ce "Honorable, ka kwantar da hankalinka, aikinmu baya buƙatar garaje da gaggawa, sai mun bi a sannu" "Haba Cp, wane irin bi a sannu? Rayuwata na cikin hatsari, yayi iƙirarin kashe ni, dole fa a nemo yaron nan, ko be kashe ni ba, idan ya buɗe bakinsa yayi wata magana a kaina kashina fa ya riga ya gama bushewa, na san fa waye yaron nan ciki da bai" Cp ya gyara zamansa ya ce "Amma honorable, wace irin yadda ko alaƙa ce tsakanin ka da yaron nan, da har ya sanka haka, zamansa a gari yake barazana a gareka" Tsaki mutumin yayi ya ce "Kai har ka tambayi alaƙar da ke tsakanin ɗan siyasa, da tantirin ɗan daba, ɗan iska? Ku nemo shi dillalin wiwi ne, da hard drugs. Da kun ganshi ma kawai a harbe shi, kuma a tuhumi controllern gidan yari, a kan dalilin sakinsa, bayan ko shari'a ba ayi masa ba tsawon lokaci" Ɗan sandan ya jinjina kai ya ce "Shi controller ya ce court order ya karɓa" "Ni dai ka yi mini wannan taimakon a nemo shi da gaggawa, dan yana cikin garin nan, tun da ga ayyukan ta'addanci yana ta yi yadda ya ga dama". CP ya ce "In sha Allah, ka kwantar da hankalinka za ayi duk mai yiwuwa, zan nemi zaƙaƙurai daga cikin mutanenmu, da suke dealing da criminal cases, very soon zai zo hannu, DSP Nasir na san zai yi abun da ya dace in sha Allah" "Yauwwa to shikenan, ko dai sanarwa za ku yi, ace duk in da aka gano shi a kamo shi, an sake shi ba bisa ƙa'ida ba" Da sauri ya ce "No ai ba haka aikin tsaro yake ba, ai wannan abun kunya ne ga hukumominmu, yanzu sanin in da yake shi ne babban target ɗinmu, dan yaron yana da wayo sosai, na bibiyi record ɗin sa, sai an yi taka tsantsan sosai wurin kama shi, sai an yi amfani da dabarun aiki, hatsabibi ne sosai" "To ayi ƙoƙarin hakan dan Allah". *** Gudu-gudu sauri-sauri ta ƙarasa gida, saboda azababben fitsarin da ya cika mata mararta, tana zuwa ɗaki ta watsar da komai a kan gadonta, ta shiga banɗaki. Sai da ta gama fitsarin, ta ji iska na shigarta, tayi wanka ta fito, ta tattare kayan da ta watsar, ta samu riga ta shan iska ta saka, ta shafa turare ta fita. Kitchen ta shiga dan zuba abinci, ta ci karo da fate-faten wake a cikin food flask ɗin ta. A ƙule ta ja uban tsaki, ta fito babban falo kamar ta fashe da kuka, ta hau ƙwalawa mai aikinsu kira. "Baba magajiya!" Daga can wani sashen ta amsa da "Na'am, Arfa gani nan" "Na ga faten wake yau?" "Eh, umarnin Hajiya babba ne, ita ta ce ayi faten wake". Cikin ɗaga murya arfa ta ce "Amma dai an san ba na ci ko? Kin dafa mini wani abun ne?" Magajiya ta ce "Wallahi har na ɗaukko doya na fara frayewa, na ɗan dafa miki, na soya miki miya, aka kuma sakani aiki". Nabila cikin kwakwazo take masifa "Saboda tsabar an tsane ni, so ake na mutu a huta, in je aiki in dawo a kasa ajiye mini abinci, sai a dafa abun da ba na so" "Ke Nabila meye haka ne, hajiya ce ta bayar da umarnin hakan, ki shiga kitchen ki dafa wani abun mana" Nabila ta kalli Yaya Sauda ta ce "In je in dawo yanzu, sannan in shiga kitchen in hau girki, bari in je in sha faten waken, duk abun da ya same ni, ku kuka kasheni, ai kun san likita ya hana ni cin wake" "To ki je ki ci ɗin mana, idan kin mutun sai ne? Banda gulma amma ai ki na cin ƙosai da shinkafa da wake, ko duk su ba waken bane ba" Kamar ƴar goye, Nabila ta din ga zirarar da hawaye ta na bala'i. "Kar Allah ya sa ki ci abun da aka dafa, kya mutu da yunwa agola ƴar wahala". Cikin tsananin fusata Nabila ta ce "Tun da dai ba shegiya ba ce ni da ubana, ai da sauƙi" Cikin son kunna Nabila, Sauda ta ce "Meye marabarki da mara uban?" Baba magajiya da ke tsaye ta ce "A'a Sauda, dan Allah kar ayi haka, ke fa babbace" Sauda ta ɗaga mata hannu tare da cewa "Babu ruwanki, ki wuce ki ƙarasawa mama aikinta. Ke kuma ki tsaya ki cigaba da hauka, banda samun wuri ina na taɓa ganin agola da miƙe ƙafa". "Ai gara ni, agolar ce, kuma iya wuya ni ƴar gari ce, ba baƙuwar haure ba, jikar yarabawa. Kuma ni ba dan albarkacin ubana ba, wallahi da na daɗe da barin gidan nan, gara na je na kama gida na yi zaman kaina, iyaka ace ina zaman kaina, ba ɗan iskan da zai takura mini" Sauda ta tsaya ta ce "To ki je ki kama ki yi zaman kan naki mana, ke dama banda Abba a tsaye yake a kanki, ai ƴar zaman kantan za ayi, kuma ƴar gagara". Nabila ta buɗe baki za ta yi magana, suka ji gyaran muryar Abba, daga saman bene. Tuni idon Nabila yayi jawur, saboda kuka da ɓacin rai. Ya ce "Magajiya" cikin sauri ta ce "Na'am ranka ya daɗe" "A gabanki kina tsaye yaran nan suke faɗa? Ki ka kasa tsawatar musu?" Ta risuna ta ce "Tuba nake ayi mini afuwa". Sauda ta ce "Wallahi Ab...." Ya dakatar da ita ya ce "Ban tambaye ki ba, kukan me ki ke yi ke kuma?" Yayi maganar yana kallon Nabila. "Faten wake aka yi, ba a dafa mini komai ba, kuma yunwa nake ji" Ya ce "Wannan abun kawai shi ne abun kuka kuma? Ke a rayuwarki ba zaki taɓa girma ba kenan?" Tayi shiru tana sheshsheƙar kuka, kukan da yake jin sa har zuciyarsa. "Magajiya, ko aikin wa ki ke yi, ki ajiye ki sama mata abun da za ta ci, ba biyanki nake dan a farantawa wani a ɓatawa wani ba, duk ƴaƴana nawa ne, babu banbanci a tsakaninsu" Ta risuna ta ce "In sha Allah Alhaji, za a kiyaye" "Ke kuma, ki cigaba da faɗa da yayyenki, zaki ga yadda zan yi da ke. Kuma na gode da furunciki Arfa, zaki yi zaman kanki ko? Tun ina raye ki ke wannan iƙrarin, ranar da na mutu ban san me zaki aikata ba, kin kyauta" bai tsaya jiran me za ta ce ba, ya wuce ya koma ɗakinsa. Sauda ta yi wa Nabila gwalo, Nabila ta ce "Ai ke yakamata na yi wa gwalo, ni na yi nasara, tun da an ce a ajiye aikin babarki ayi nawa, banza ƙatuwar kwabo" Nabila ta wuce ɗakin su, tana tunanin ko dan wannan tijarar, ya isa tayi fatan tayi aure ta bar gidan nan. *** Ɗan siririn matashi ne dogo, wankan tarwaɗa, sanye da kakin ƴan sanda, da ɗan hanzari yake bin wata doguwar baranda, wadda ta sa da shi da wata ƙofa. Ya buɗe ya shiga da sallama, ya sarawa wanda ya tarar a cikin ofishin, wanda da gani babu tambaya, ka san babba ne sosai a cikin rundunar jami'an tsaro, duba da yanayin ranks ɗin da ke maƙale a kafaɗar uniform ɗin sa, da kuma haɗuwa da tsaruwar office ɗin na sa. Ya ƙame tare da sarawa mai office ɗin, ya yi masa alama da ya zauna. Ya zauna tare da sake gaida wanda ya tarar a office ɗin, da uniform ɗin sa ke ɗauke da sunan ACP Solomon wada. ACP wada ya kalli matashin ya yi murmushi ya ce "CSP Nasir Yusuf" Nasir ya waro ido ya ce "Wane ni Yallaɓai, Dsp ɗin dai" "Au Csp ɗin ne ba ka so? Ba abun mamaki ba ne ba, ka ji gobe kai ne Cp na garin nan, kai koma IG gaba ɗaya" Nasir yayi murmushi yana sunkuyar da kai. "Ƙwazon mutum babu in da ba ya kai shi, kuma kar ka yi mamakin ƙwazonka ya kai ka in da ba ka zata ba. Yanzu ba karatunka da kuma ƙwazon ne ya kawo ka matakin da ka ke yanzu ba?" Ya jinjina kai ya ce "Haka ne ranka ya daɗe". Acp Wada ya ce "Good, wani aikin za'a sake baka, wanda mu ke buƙatar sa da gaggawa, direct order ce daga Cp,ya kuma ce a jinjina maka aikin office ɗin ka yana kyau" Nasir ya tattara hankalinsa ya ce "Ok sir, na gode sosai" Solomon wada ya ce "Nasir, idan ka mayar da hankali yadda ake so, ka gudanar da aikin nan, za ka samu cigaba a aiki sosai da sosai" Cikin girmamawa ya sake cewa "I will do my best in sha Allah". "Good" ya ɗaukko wani file ya ajiye masa, sannan ya ce "Kwanakin baya, akwai wani ɗan daba, da ya addabi garin nan, kai ɗan garin nan ne za ka fi ni sani, wai shi Aminu ana yi masa laƙabi da viper. Shekarun da suka gabata yana tsare, sakamakon laifin da ya aikata, kafin kwatsam mu samu sanarwar cewa an sake shi. So bayan sakin nasa, akwai kokwanto a cikin sakin da aka yi masa ba bisa ƙa'ida ba ne ba, duk da controllern gidan yari ya ce order aka bashi ya sake shi, bayan fitowarsa ya cigaba da aikata miyagun laifuka a ɓoye, na sayar da miyagun ƙwayoyi tare da ƙyanƙysar sabbin ƴan daba, da suka hana jama'a zaman lafiya a garin nan, wanda yaƙi da wannan a ƙarƙashin kulawar office ɗin ka yake, a zone ɗin. Abun da muke so da kai shi ne, Aminu ya shigo hannu, ko ta halin ƙaƙa." Nasir ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Ok sir, tabbas cases na dillancin ƙwayoyi da harkar daba, yana ƙara ta'azzara, amma laifin me yayi aka kai shi kurkuku? Kuma ya aka yi, aka sake shi ba bisa ƙa'ida ba?" "Wannan ba huruminka bane ba, duk ba shi ne a gabanmu ba, kamo yaron shi ne abun da muka saka a gaba, wannan abun da ya shafi shari'a ne, ɓarnar da yake aikatawa ta yi yawa. Kuma a zone ɗin ka yaransa suka fi yawa, dan haka ka je ka yi iya ƙoƙarin ka a kai. Yabawa da nustuwarka, da jajircewar ka ya sanya muka baka aikin nan, ina nan ina saurarenka, ba a buƙatar ɓata lokaci. Ka je ka duba file ɗin a tsanake, akwai sauran informations da za su taimaka maka wurin kama yaron, da duk wani record na criminal acts ɗin sa yana ciki. Nan da gobe in Allah ya kaimu zaka dawo mini da file ɗin. ba na buƙatar kuma ka yi wani abu sama da haka, kar ka ƙetare iyakar da na gindaya maka". "Ok sir, i will do mai best in sha Allah" ya ɗauki file ɗin, tare da sake sara masa ya fita. Ɓangaren Nabila kuwa, al'amuranta ba a samu sauyi ba, dan duk shari'ar da ba ta yi mata ba, ba za ta mayar da hankali a kai ba. Director kuma ya bar ta ne, saboda mutuncin mahaifinta Major Yusuf da yake gani, mutum ne na gari kuma akwai tarin alkhairai da ya yi masa, shiyasa ya ƙyale Nabilatake cin karenta babu babbaka. Nabila gaba ɗaya wasu lokutan sai ta ji tana danasanin karantar ɓangaren shari'a, yadda wasu abubuwan suke gudanawa sam ba sa yi mata daɗi. Hausawa suka ce sai hali ya zo ɗaya ake abota, ɓangaren ƙawarta sumayya ma haka, kusan ƙalubale ɗaya suke fuskanta, dan har gara ma Nabila tana da alfarma a wurin na ta aikin, Sumayya kuwa na ta babu sani babu sabo. Yau ganin motar Abba a gida bayan ta dawo daga aiki, ya sanya ta fuskanci yana gidan, dan haka da ta zuba abincinta, sai ta hau saman benensa. A falonsa ta tarar da shi da Yaya Nasir, suna magana, da alama magana ce mai muhimmanci suke yi, sai dai yayi shirin fita. "Abba sannu da gida" "Yauwwa" ya amsa a taƙaice. Sai dai ta na zama ya tashi ya yi wa Nasir sallama, ya fita ya bar falon. Nasir ya galla mata harara. A shagwaɓe ta ce "Dsp me na yi ne? Kwana biyu duk Abba ya canza mini, kai ma kuma kana hararata" "Ba dole ya canza miki ba, duk kin gallabi kowa a gida, bayan na dawo daga kaduna ake gaya mini wai kin je biki kin yi dare, ƙarshe a haraba ki ka kwana yayi punishing ɗin ki, ba ki zo kin bashi haƙuri ba. Law firm ɗin ku director ya kawo masa ƙara, daga danna waya sai kwalliya ki ka iya, ba kya son aiki, yayi ta bashi haƙuri ya ce a kula da ke a koya miki aiki, ko ba a biya ki ba, shi zai din ga biyanki salaryn. Kwatsam jin kunnensa ya ji ki na cewa ba dan shi ba, zaman kanki zaki yi, kin san kwana nawa ya ɗauka ba ya bacci saboda wannan maganar da ki ka yi? Duk cikinmu babu wanda Abba yake lelensa kamar ke, amma sai ba shi kunya ki ke ko ta ina?" Cikin sanyin jiki, da tashin hankali ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ban zaci ran Abba zai ɓaci har haka ba, to kuma ba ka bashi haƙuri a madadina ba? Yaya sauda ce fa take ce mini agola, ni kuma ba na son na gaya masa. Ba na son fushin Abba, dan Allah ka tayani ba shi haƙuri. Maganganun Sauda ne suka ɓata mini rai, na yi dana sanin abun da na faɗa, amma dan Allah Yaya Nasir ka bashi haƙuri" Ya girgiza kai ya ce "No ni ba ruwana" Kuka ta saka masa tana cewa "Wallahi ba zan ci abinci ba, sai yanzu na ji maganar da na yi, ta yi nauyi ban san abba zai ji ba" "Kin ga ya isa, kar ki saka ciwonki ya tashi na shiga uku, ya mayar da fushin da yake yi da ke kaina" ai kamar ya sake tinzirata, ta cigaba da sheshsheƙar kuka. Cikin tsawa ya ce "Ke wai dan ubanki meye haka? Am i your mate, ba magana nake yi miki ba?" Sai da ta razana, amma hakan bai saka ta daina kukan ba. Ya zuba mata ido, Nabila tun asalinta tun tana yarinya take fama da taurin kai na tsiya, yanzu ko dukanta zai yi, ba za ta daina kukan da take yi ba, balle ma yanzu ba wannan dan ta girmi duka. Har mamakinta yake yi, ƙatuwar budurwa ta kammala degree, kusan shekara ashirin da huɗu amma tana abu kamar yarinya ƙarama. Tsaki yayi, ya tashi shi ma ya fice, ya ƙyale ta, ta ci uban kukanta, ta kwanta a kusa da flask ɗin Abincinta ta hau baccin gajiya. A tsanake Nasir yake duba file ɗin da aka bashi, a kan Aminu viper, da aka ce lallai ya kamo. A record ɗin da ya duba, ya gano zuwan Aminun gidan yari, ba sau ɗaya bane ba, a kan mabanbanta laifuffuka da suke da alaƙa da harkar daba, da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi. Sai dai abun da ya ɗaure masa kai, ba a shigar da dalilin da ya sanya, aka kai shi prison na ƙarshe ba, an dai nuna ya aikata wani babban laifi ne, da ga cikin manyan laifuka da bai kamata daga lokacin faruwar abun zuwa yanzu ace an sake shi ba, haka zalika an cire wasu abubuwa masu muhimmanci da yakamata ace ya gani a cikin file ɗin, sannan ga shi solomon Wada ya yi masa umarni da ya yi amfani da iya abun da aka bashi. "To menene dalilin haka?" Ya tambayi kansa, a lokacin da kan na sa ya ƙara ɗaurewa. Sake duba file ɗin yayi yana tunani, kamar ya taɓa duba wani case, makamancin record ɗin da yake cikin file ɗin, sai dai kamar sunan ba haka yake ba. "Aminu Viper" ya sake maimaitawa. Ayshercool. 08081012143 [7/17, 1:25 PM] null: ⚔️*ƘARFE A WUTA ⚔️ AISHA ADAM AYSHERCOOL https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g 3 Sama-sama Nabila ta ke jin hayaniya a kanta. Amma ta ƙi motsawa. "Ke Arfa" yayi maganar yana riƙe hannunta. Tashi ta yi zaune tana buɗe idonta a kan Abba, a sanyaye ta ce "Abba ka dawo?" "Na dawo, tun da na tafi ki ke kwance a nan, ko abincin ba ki ci ba?" "Abba Yaya ne ya ce kana fushi da ni, dan Allah ka yi haƙuri ba zan sake ba" Major ya ce "Eh ya kira ni ya gaya mini, na haƙura tashi ki wanke fusarki ki zo ki ci abincinki" ta tashi ta shiga banɗakin falon, ta wanke fuskarta, ta zo ta zauna ta saka spoon ta fara cin abincin. Ya numfasa ya ce "Rashin ji ne, ya yi miki yawa arfa, duk yadda na so na yi haƙuri sai kin ƙure ni, ban bi daɗin abun da kunnuwana suka jiye mini ba, kina iƙrarin zaki yi zaman kanki" "Abba ka ce fa ka haƙura, ba zan sake ba" "To shikenan na ji, ci abincin" Umma tayi sallama da flask ɗin shayi, matarsa ta biyu, kasancewar yau girkinta ne. Ta zauna a kusa da shi, ta haɗa masa tea, ya karɓa yana sha ya na yi wa Nabila hira, kamar bai yi fushi da ita ba, har ta ɗan ware. Kiran sallar magariba ne, ya sanya ta tashi ta bar ɗakin, dan umma ta ji haushin zaman da Nabila ta yi, ita kanta Nabila ta so ba su wuri, amma Abba ya cigaba da jan ta da hira. Da ya dawo daga sallar magariba, kai tsaye ɓangaren mama ya wuce, tana zaune a falonta, da Sauda su na kallon tv. Gyaran murya yayi, sannan yayi sallama, suka amsa suna yi masa sannu da zuwa. Ba tare da ya amsa ba ya kalli Sauda ya ce "Sauda nan gidan waye?" Ta ɗan yi turus tana kallonsa. "Ki amsa mini" "Gidanka ne Abba" Ya ce "Masha Allah, idan ba zaki iya zama da ni, da tsarina ba, ko ki koma gidan tsohon mijinki, ko kuma ki fitar da miji ki yi wani auren" Cikin damuwa Mama ta ce "Major me yayi zafi haka?" "Baƙar aƙidar ki, da ta ara ta yafa, ba zan lamunta ba. Kun sani ba na ɗaukar duk wani abu da ya shafi Nabila da sauƙi, yadda na yi mata shamaki, da wanda ya zama katangar rayuwarta, dole na tsaya tsayin daka, na kula da ita kamar yadda na yi alƙawari. Ba zan lamunci a cigaba da wulaƙanta mini ƴa ba, har ta fara iƙirarin za ta yi zaman kanta. Babu wani ɗa da ya fi Nabila a cikin gidan nan, idan ki ka sake ce mata agola, to zaki fita ki bar mini gida ki nemi wani uban". Cikin takaici mama ta a ce "Amma da kunnenka ka ji ta faɗa mata haka? Ka san dai makirci irin na yarinyar nan ko?". "Kunnena ne ya jiye mini, ko zan yi mata ƙarya ne?" Suka yi tsur-tsur baki daya. Ya ja guntun tsaki ya bar falon. Yana fita sauda ta ce "Mama dan Allah sai yaushe Abba zai daina fifita yarinyar nan a kanmu, tun da aurena ya mutu bai taɓa yi mini gori ba sai yau, saboda ita?" "Ba ke kaɗai ba, ni kaina yadda ki ka san na yi mata kucciya, duk ita ce matsalar gidan nan, amma zan kawo ƙarshen komai da kaina, ki bar ni da su". Nabila kuwa na ɗakinta, itakaɗai, tana duba document ɗin shari'ar da director ya saka aka ba ta, sai dai gaba ɗaya ba ta da intrest a kan shari'ar, da ta gaji ma, ajiyewa ta yi ta hau waya da saurayi. Wata matashiyar budurwa ce ta shigo ɗakin ta ce "Wallahi Nabila abun da ki ke yi ba kya kyautawa" Nabila ta ɗan kalli Asiya, ta katse wayar ta ce "Da na yi me?". "Kin saka Abba ya yi wa mama da Anty sauda kaca-kaca saboda ke, sai da Anty sauda ta yi kuka". "To ai cewa zaki yi, Abba bai kyauta ba ni meye nawa a ciki?" "Amma ke ki ka gaya masa ta ce miki Agola, bayan yayi musu mu ma ya iskemu a babban falo, ya yi ta yi mana faɗa". Nabila ta ce "Ashsha, ai kin san ni bana kai ƙara, ko dai na ɗauki mataki, ko kuma Allah ya saka mini da gaggawa" Asiya ta ce "Ai shikenan, kowa yayi na gari kansa". Nabila ta ce "Allah ya yaye miki Aisya, ke ma fa matar nan idan ta tashi karta miki wulaƙanci, ba saurara miki take yi ba, daga ke har umman, amma ku yi ta bin ta kamar wata shugaba, ni dai ba mai takani ban ɗaga ƙafar na karya ba" "A'a ai ke ki ka ce, ke ki na da ma dogara" Nabila ta yi tsaki, tare da furta "Allah ka aurar da ni na huta da wannan kacaniyar gidan, Ya Allah dogo mai gemu" ta fita daga ɗakin tana addu'a. Bayan kwanaki takwas. A tsaye yake ƙyam, kamar ƙofa, kasancewar in da yake a tsayen ba a iya ganinsa sosai saboda duhu, sai dai inuwarsa ta nuna dogon mutum, kakkaura. Ya ɗauki ɗankwali, ya ɗaure kansa da shi, tare da naɗo ɗankwalin ya rufe fuskarsa sai idanunsa kawai ya bari a waje. Ya laluba hannunsa, ya ɗaukko wata irin doguwar wuƙa, ɓangare ɗaya zarto, ɗaya kuma kaifi, ga ta da uban tsini, a ƙalla za ta yi kamu uku, ya ɗaga rigarsa ya soketa. Ya sake ɗaukar wata ya soke a jikin wandonsa. Yanayin takun da yake kawai, ya isa ya tabbatar daƙaƙarfa ne, saboda yadda ƙasa ke amsa takun nasa. Bayan wasu awanni, duhun dare ya ƙara yi, sahu ya ɗauke, sai haushin karnuka ko ina. A ƙofar wani gida ya tsaya, ya din ga waige-waige, ya tabattar da babu kowa. Tamkar ɗan biri, haka ya cafke katangar gidan ya dira ciki. Ya saka mukulli, ya buɗe wata ƙofa a cikin gidan da duk ta yi ƙura, ya buɗe ta ya kutsa kai ya shiga ciki. Tsayawa yayi ya kunna fitilar wayarsa, yana haske ɗakin, take ya ji wani abu mai tsananin ɗaci ya fara kaiwa da komowa a ƙirjinsa, ya ji numfashin sa na barazanar barin ƙirjinsa. Jikinsa ne ya fara rawa, ya ji tamkar hankalinsa zai gushe, ya durƙusa a wurin yana wani irin haki, cike da wani yanayi na mai shirin fita hayyaci. Hayaniya ya fara jiyowa a waje, hakan ya saka shi miƙewa tsaye babu shiri. Cikin sauri ya fito daga ɗakin, ya kama katanga, ya leƙa, sai dai yana leƙawa ya ga ƴan ƙato da gora da miyagun makamai, sun fara taruwa a kewayen gidan, kasancewar akwai hasken farin wata, kuma akwai hasken ƙwayayen solar hakan ya bashi damar ganin makaman da suke hannun su. Babu tsoron komai, ya haye katangar, ya hau saman roofing gidan, ya dira ta wani ɓangaren, jin sautin dirarsa, ya sanya suka rufa masa baya, ta in da suke jiyo sautin gudunsa har da karnuka su na kururuwar a tare. Sai dai duk da wannan ƙira da Allah ya yi masa, ta siffar ƙarfi ba ya jin nauyin jikinsa, ya din ga dukan ƙasar da dukkanin nauyin jikinsa,  ba su ankara ba, ya ɓace musu ɓat kamar walƙiya. A bakin titi suka tsaitsaya suna haki, su na mayar da yadda aka yi. Ɗaya daga cikin su ya ce "Anya yaron nan, ba da layar zana yake amfani ba?" "Ba wata layar zana, tsohon hatsabibi ne kawai, ni na yi mamaki ma da ya gudu ai, da da ne fa, wallahi sai ya illata ku kan ya gudun. Ai kamar yadda na gaya muku ne, da na ji alamun ya zo, zan kira ku a waya na sanar muku, ai ba zan sake sukuni ba sai ya je hannu, na za ta ma zaku kira ƴan sanda ne" Ɗaya daga cikin jami'an sintirin, ya ce "Ko zamu kira ƴan sanda, mu yakamata mu fara huɓɓasa mu kama shi, sai mu miƙa musu shi, wannan gudun nasa yaushe muka kira ƴan sanda ma" "Amma duk da haka, yakamata su san yana zuwa ai" Shugaban su ya ce"Muddin suka sani, canza taku zai yi, ba zai sake zuwa ba". Malam lawan da gidan sa ne a jikin gidan da yake zuwa ya ce "In ji wa? Ba zai taɓa iya daina zuwa gidan nan ba, yadda ka san ya binne asiri a ciki, kodayeke sai ta yiwu ma asirin ya binne, wannan hatsabibancin nasa akwai lamarin sihiri a ciki, amma zan cigaba da saka ido, da ya zo zan kuma kiranku" "To shikenan malam lawan mun gode, yanzu ka koma gida, bari mu koma bakin aiki, ko kuma a raka ka ne?" "Ahha haba, kamar ba namiji ba, ba wani abu bari na koma, ai ya riga ya gudu" Suka yi sallama ya nufi layinsu. Sai dai yana daf da ƙarasawa gidansa, kawai ya ji an yi ball da shi, kasancewar sa ɗan ƙaramin mutum, sai jin sa yayi, ya yi sama ya dawo ƙasa kamar wani karmami. Ya tashi a gigice yana zaton ko gamo yayi da aljani, ya hau waige-waige. Haske shi ya yi da fitila, sannan ya ce "Kwana da yawa malam lawan, tsohon butulu, da na ƙyale ka ban yi maka komai ba, shi ne ka cigaba da yi mini bita da ƙulli?" Cikin kwakwazo, da tsananin razani ya ce "Na tuba, na bi Allah na kuma bi ka, dan Allah" kan ya ƙarasa, ya karya shi ɓaras, ta hanyar saka ƙafa, ya yi masa wani irin duka a ƙafarsa ɗaya. Malam lawan ya a kurma ihu, cikin tsananin zafin nama, ya cire hular kan malam lawan,, ya tura masa a baki, sannan ya ciro wuƙar ƙugunsa ya yanke shi a damtsensa, aikuwa jini ya ɓalle. Ya durƙusa a gaban sa ya ce "Yanzu ai ka ji daɗin bayar da rahoton zuwana, ragon maza kawai" ya tashi tsaye ya ja da baya ya ɓace a cikin duhu, ya bar shi a mawuyacin hali, ga karaya ga yanka, gashi kuma ya toshe masa baki. Ko da ya koma gidansa da yake zaune, ciro wuƙar da ya yanki malam lawan yayi, yayi jifa da ita. Ya tsaya yana haki, abun da ya yi alƙawarin dainawa, yau ya yi, ya zubarwa da wani jini. Ya dafe kansa yana huci cikin tsananin damuwa. ** Yau sumayya ba ta haɗa tafiya da Nabila ba, dan da wuri sosai ta fita, za ta shiga asibitin murtala ta duba wata yayar babansu da aka kwantar a emergency, za ta kai musu abinci. Su na tafe da mai adaidaita sahu, ta hango mutane na ta shiga su na fita a wani layi, duk da lokacin gari bai gama hasken da za ace, mutane suna wannan tururuwar ba. Da sauri ta tsayar da mai baburin, ta biya shi kuɗinsa, ta  sauka, ta nufi layin da mutane ke shiga su na fita. Wurin duk babu mata, sai maza, amma hakan bai hanata kutsawa da son gano abun da yake faruwa ba. Tsayawa ta yi ta tambayi wani magidanci, abun da yake faruwa. Ya sanar da ita, gawar wani yaro aka tsinta, a bayan maƙabartar unguwar, an yanke masa al'aura da wasu sassa na jikinsa. Jikinta na tsuma ta cigaba da kutsawa tana faɗin "Ku matsa, ni ƴar jarida ce" tare da nuna musu id card ɗin ta. Ta ɗaɗɗauki hotunan yaron, sannan ta tsaya tattaunawa da mutanen da suka fara zuwa su ka tarar da abun. Sai kiranta ake yi a waya, ana jiran ta kai abinci, amma sai da rana ta ɗaga sosai, aka gama komai ƴan sanda suka zo, sannan ta yi shirin tafiya, shi ma sai da ta karɓi lambar wayar wani ɗan sanda, da zimmar zai din ga ba ta update na sakamakon binciken da za su yi, a kan gawar. Ko da ta je asibiti ta sha faɗa,na rashin kai musu abinci da wuri, ko a jikinta, saboda ta samu rahoto, dan haka tana ajiye musu abincin, ta yi waje. Sai dai ba ta fito daga emergency ba, ta din ga jin ihun wani babban mutum, kamar mara gaskiya, haka ta koma tana leƙawa ta ga abun da yake faruwa. Magidanci ne, ake yi masa ɗinkin wani uban yanka a damtsensa, jikinsa yayi kaca-kaca da jini, duk da ana ta yi masa allaurar kashe zafi, amma sai ihu yake yi. Babu neman izni, ta afka ciki ta ce "Sannu bawan Allah, ka yi haƙuri Allah ya baka lafiya, ka daure" Duk sauka waiwayo su na kallonta, har da ma'aikatan, mutumin ya ce "Na gode sosai" Ta ƙara matsawa ta ce "Amma hatsari ka yi ne? Kodayeke wannan ai yankan makami ne ba hatsari ba" Ya ce "A'a wani ɗan daba ne, ya sare ni jiya cikin dare, dama hukuma ta daɗe ta na neman sa" Sumayya ta gyara tsayuwarta ta ce "Subhanallah, bawan Allah a wace unguwa ce haka? Ko rigima ku ka yi da shi ne?" Ƙanin malam lawan da yake tsaye a wurin, a fusace ya kalli sumayya ya ce "Dalla malama fita, mutum yana fama da kansa, kin zo ki na yi masa wasu surutan banza" Ta ce "A'a Allah ya baka haƙuri, ka sani ko akwai wani taimako da zan iya yi masa. Kalli saran da aka yi masa fa, idan ba za ka damu ba, zan naɗi muryarka, mu saka a radio, ko Allah zai saka, hukuma su bi maka haƙƙinka, barin su da ake yi suna cin bulus ya sanya suke cigaba da ɓarna". Malam lawan ya ce "Ke rufawa kanki asiri, hatsabibanci da ta'addanci yaron, ya wuce tunanin ki" Sumayya ta zaro wayarta, za ta yi magana, sai ga wasu mutane guda biyu sun shigo da wani kaki a jikinsu, da ba ta san na menene ba, suka mayar da ƙofar ɗakin suka rufe. Malam lawan ya kalle su, ba su ne ƴan sandan da aka kirawo suka tsaya masa, likitoci suka zo kansa ba ne. Sumayya ta yi tsilli-tsilli da ido,  ɗaya ya ƙirga mutanen da suke cikin ɗakin, da likita ɗaya, nurse ɗaya, sai ƙanin malam lawan da sumayya. Dan duk maƙwabtan da suka kawo shi, sun tafi wurin sana'oin su. ya ce "Ku biyar ne a ɗakin nan, idan ka sake mu ka ji labarin sunan wanda ya yi maka wannan raunin, to za ka maye gurbinsa da ya bari na gidan yari, dan haka ka ja bakinka ka yi shiru". Sumayya ta ce"Ban gane ba Yallaɓai, mutum mai laifi kuma ace kar a faɗi waye? Ba ka ga irin illar da aka yi masa ba ne, ga karaya ga rauni, da ya kashe shi fa?" Ya ba ta amsa da "Da ya kashe shi, bakinki zai iya sakawa, ki ɗauki hukuncin da za ayi masa na kisan" daga nan suka juya suka fice. Mamaki ya mamaye sumayya, ta ce "Kai kuwa bawan Allah, waye wannan shi kuwa, da har jami'an tsaro masu kaki, za su hana bayyana laifinsa, ana sane aka ƙi kama shi kenan?" Malam lawan ya ce "Ba zaki ja mini masifa ba, ki fita ki bar wurin nan, na ji da masifa ɗaya, bayan ɗinkin nan a karye nake wallahi" Cikin tsananin naci, da son samun rahoto, ta kwantar da murya za ta lallaɓa shi, ta samu labari, amma da likitan da ƙaninsa suka koreta daga ɗakin. Fitowa ta yi, tana ta mamakin abun da ya faru, yaya za ayi hukuma ta bawa mai laifi kariya, wane irin abu ne haka?. Ba ƙaramar makara ta yi ba, amma tunanin abun da ya faru, ya fi ɗaure mata kai. *** Sannu a hankali yake yi wa kansa allura, yana yi yana fatan samun abun da yake so, a hankali ya gama ɗurawa jijiyarsa ruwan allurar da yake fari tas a cikin sirinji, bayan ya kammala tsaf ya fara jin kansa yana yi masa nauyi. Take idanunsa suka yi mitsi-mitsi, ya soma lanƙwasa kansa, yana jin idanunsa kamar za su fito waje, suna yi masa yaji, a haka ya kunna sigari, ya kashingiɗa, ya na bawa sama hayaƙi,yana jin yadda jikinsa ke son bijirewa aikin allurar. Wayarsa ce ta fara vibrating, ya miƙa hannu, ya ɗaukkota ya duba, yana zaton ko a cikin yaransa ne, sai dai ya ga private number ce. Har zai ƙi ɗagawa, sai kuma ya ɗaga ya saka a kunnensa, amma bai yi magana ba. Daga cikin wayar aka ce, "Meyasa ba ka gajiya da neman magana ne? A wannan karon ma sai da ka saka na yi abun da na goge ɓarnar da ka yi, yakamata ka nutsu Aminu" Ya saki hayaƙi, tare da ɗan kaɗe tokar da sigarin ta tara, sannan ya ce "Waye kai? Sannan waye ya saka?" Mutumin yayi dariya, ya ce "Mutum mai ba ka kariya, domin cimma nasa muradin, yakamata ka sauƙaƙa mini aiki, ka daina aikata abubuwan da za su din ga barin trace a kan ka". "Ka yi muguwar kasadar ƙoƙarin cimma burinka da mutum irina, kar ka manta viper ake yi mini laƙabi da shi, macijin da ya fi kowanne hatsari, idan ka bari na sare ka, ka gama yawo" yana gama maganar ya cillar da wayar, ya ɓata fusaka kamar ya fashe da kuka. Cikin fusata ya ce "Ni again? wani ya kuma amfani da ni? Impossible zan watsa dafina a in da ya dace da in da bai dace ba, sai na tabattar da danganawa ga kunyar ƙarshe, ko da kuwa za ayi mutuwar kasko" ya yinƙura da nufin ya tashi tsaye, amma ya kasa sarrafa gangar jikinsa, hakan ya tilasta masa komawa ya nemi wuri ya kwanta. Duk da irin faɗan da sumayya ta sha a wurin aiki a kan makara, bai dame ta ba, jikinta sai tsuma yake saboda ta zo da rahotanni masu muhimmanci da ɗaukar da hankali. Ofishin head of news ta je, ta shiga da sallama. Matar ta ɗago ta amsa mata da ƙyar, ta ƙarewa sumayya kallo, ta ce "Yanzu ne lokacin shigowa aiki ko? Gaba ɗaya yaran yanzu ba kwa ɗaukar aiki da muhimmanci, kodayeke karatun ma ba wani na kirki ku ka yi ba, duk da satar amsa ku ke gamawa. Ki shiga hankalinki kafin na kai maganar nan wurin MD" Sumayya ta risuna ta ce "Afuwan anty, in sha Allah ba zan sake ba, na samu wasu rahotanni ne masu muhimmanci, da ya san na tsaya a hanya, shiyasa na makara na kawo miki a tantance ne ko za a saka su a news" A yamutse matar ta ce "Na menene" cikin farinciki da jin ƙwarin gwiwar ta yi abun arziki ta fara da gaya mata abun da ya faru a asibiti. Amma matar sai cewa ta yi"Amma ba ki da hankali ko? Ta yaya zamu saka wannan shirmen a news?" "Anty ai a rahotanni, ko a janyo hankalin hukuma.... "Dalla yi mini shiru, business mu ke yi a nan mu, ke fa iyayinki da rawar kanki yayi miki yawa sumayya. Meye hujjarmu idan aka tsutsiye mu, cewar hukuma na ɓoye mai laifi?" Sumayya ta ce "Wallahi a gabana aka yi, mutumin yana nan a emergency" "Kin ga idan ba ki da abun faɗa, fita ina da abun yi" Sumayya ta yi iya ƙoƙarin ta, ta danne abun da yake taso mata na fushi ta ce "To shikenan, sai kuma akwai abun da na gani, ina kan hanyar tahowa nan, a nan wajen gari, an tsinci gawar yaro an cire masa wasu sassan jikinsa". "Almara kenan, wa zai yadda da wannan zancen?" "Ba zance ba ne ba, na yi recoding ɗin maganar wasu daga mutanen da suka fara cin karo da abun". "Sumayya, ba irin wannan labaran mu ke buƙata ba dan Allah, je ki su murtala sun fita neman rahotanni, ki din ga kawo sensitive abubuwa" Summaya ji tayi wata irin ashar na kai komo a wuyanta, da take ƙoƙarin narkawa matar nan, ta rasa abun da ta yi mata, haka kurum ta tsane ta. Ta yi ta kyararta ba ta son ta ga tayi wani abu na cigaba. Sumayya ta fice daga office ɗin kamar ta yi kuka, ta koma reception ta nemi wuri ta zauna. Ba uwar da ta tsinana a aikin yau, tun da head of news department ta yi mata wulaƙanci. Kasancewar a makare ta je, ya sanya lokaci yayi gudu, Lawisa, wato head of news ɗin, ta din ga shiga tana fita, ta na kaiwa tana komowa, idan ta kalli in da Sumayya take sai ta haɗe rai. Wannan karon bayan ta fita, a tare suka shigo da managern director, sai karairaya take yi masa, tun da ya shigo ma'aikatan suke ta gaishe shi. Ban da sumayya da ɓacin rai ya saka ta cika ta batse. Sai da yayi gyaran murya ya ce "Wannan ba sabuwar staff ɗin mu ba ce? Ya na ganki a nan? Wane department aka kai ta ne?" Lawisa ta yi caraf ta ce "Sir ba ta da ƙwarewar aiki ne haryanzu, ana ɗan nunnuna mata aiki ne, kafin ta gama gogewa". Ya ce "Ok, babu laifi" sumayya kamar ta kwaɗawa lawisa mari, a fusakarta da ta sha uban bleaching, duk tayi taruwar jini. Ta daure ga gaida MD, sannan suka wuce gaba. Tsaki Sumayya ta ja, tana duba wayarta. Sai dai jin sallamar Nabila a reception ya sanya ta ɗago da sauri tare da amsa mata. "Ya na ganki a nan?" Nabila ta ce "Ke baki iya karrama baƙo ba ko?" Ta tsaya suka gaisa da admin ɗin da ke reception, sannan ta ƙarasa kusa da Sumayya ta zauna. "Arfa, ya na ganki yanzu ne? Lokacin tashi daga aiki bai yi ba?" "Kema ya na ganki a nan kamar mara galihu, ke baki da office ɗin da zaki zauna ne? Ki zo chambermu ki ga ofishin da aka bani hajiya, kamar wata sarauniya" Sumayya ta ce "Eh ofishin da baki damu da aiki ba ko, sai sun dawo da ke gadin chamber tukuna". Nabila ta yi dariya ta ce "Kin san wani abu, wai nan aikena aka yi, zan je na lallaɓa na zo da wata mata, ko in tattauna da ita, sannan in je shagari firm, zan haɗu da wani lawyer, kuma ni wallahi kaina ciwo yake yi" Sumayya ta kalleta ta ce "Ba zaki ba kenan?" "Ai faɗa ma ɓata baki ne, sumayya wurin nan naku mai kyau, tashi ki rakani na zaga" duk da ran sumayya babu daɗi, amma ganin Nabila ya sanya ta jin sanyi a zuciyarta. Suka shiga zazzagawa, ta kaita news room, sai dai su na buɗewa suka tarar da MD da lawisa a ciki, suna aiki. Sumayya ta risuna ta ce "Am sorry sir, ban san ku na ciki ba, Arfa mu je ki ga.... "A'a tsaya mana na ga nan ɗin, Nabila ta shiga cikin fara'a ta ce "Yallaɓai ina wuni?" Shima cikin fara'ar ya ce "Lafiya ƙalau, ya ki ke?" "Lafiya lau sir, ina fatan ba zan takura muku ba, ina son sanin abubuwan da ban sani ba a rayuwata, mussaman wanda ba field ɗina ba, sister ina wuni?" Tayi maganar tana kallon lawisa da ta yi bala'in haɗe rai. Lawisa ta takurawa Sumayya ne, saboda tana ganin ƴar gayu ce, ga ta baƙa amma baƙinta mai kyau ga ƙwazo, tana gudun ta ƙwace mata matsayin ta, kuma ita bazawara ce, a da a wurin babu wanda ya kaita gayu a wurin, amma yanzu sumayya ta fita. Yanzu kuma ga Nabila, ita da take da hasken fata ma sosai. Nabila ba ta san lawisa ta amsa ko ba ta amsa ba, ta ja kujera ta zauna, tana yi wa MD tambayoyi, a kan abubuwan da suke cikin news room ɗin. Lawisa ta ƙulu,ta din ga harar Nabila, amma ko a jikinta, ita kanta sumayya sai da haushi ya kamata abun da Nabilan take yi. Nabila ta ce "Yallaɓai, ko zaka saka mini lambarka, idan wani abu ya kama na aiki, zan iya taimakawa i am barrister Nabila Yusuf" Ya ce "Wow, what a very young and beautiful barrister, kin zama lawyer da ƙananan shekaru, ya karɓi wayar Nabila, ya saka mata lambarsa, ta tashi ta yi musu sallama. Sumayya kamar ta yi bindiga, su na fita ta din ga ɗurawa Nabila ashar, a kan abun da ta yi, tare da gaya mata alaƙar Lawisa da kuma MD. Nabila ta ce "Sumayya, dan Allah kar ki ɓoye mini, idan yana da kuɗi na ci rabona, na ga zai yi son mata" Ganin Nabila na neman mayar da ita mahaukaciya, sai ta canza maganar. "Ke kin san menene? wai ni zan kai rahoto har kashi biyu, sakaryar matar nan ta ce ba za a saka ba, wai ba sa buƙatar irin wannan labarin, MD ya tambayi me nake yi a reception ba na aiki, wai ta ce masa ban iya aiki ba, na rasa uban da na tsare mata ta tsane ni, dama ni na samu damar da ake baki, a wurin aiki, in yi wata shida ina aiki a wurin, wai ban iya aiki ba, da yake kwanan nan ya dawo daga ƙaro karatu, tun da aka ɗaukemu ya tafi". Maimakon Nabila ta tausaya mata, sai ta hau dariya, "Ai kawai ki fara soyyaya da MD ko ta bala'i, shi ne zaki rama". Sai da ta ga Sumayya ta yi fushi sannan ta ce "Sorry my sumy, maganar gaskiya babu daɗi, kuma kishi take da ke kuma tana ƙoƙarin kare abun da take so, shikenan" Idon sumayya ya tara hawaye ta ce "Sai kuma ta din ga daƙile ni a harkar aikina? Ta yi mini adalci kenan?" Nan ta ba wa Nabila labarin abun da ya faru, daga fitowarta daga gida, zuwa yanzu. Nabila ta ce "Na shiga uku, sumayya me ƙasarmu ke son zama ne? A zahiri an nunawa mutane ana neman mai laifi, a baɗini kuma hukuma na ɓoye shi? Duk yadda ake fama da ƴan daba da masu ƙwace a garin nan, tirƙashi ana maganin ƙaba kai yana daɗa kumbura, ke ba ki san sunan wanda ya yi laifin ba?". Sumayya ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, bai faɗa ba, korata ma suka yi". "Mu ƙarasa titi mu tari napep mu je asibitin, mu tattauna da shi mutumin, ni kin san ba na tsoron a mutu ko a yi rai. Sannan zan je na samu Yaya Nasir na yi masa maganar wannan ai abun kunya ne" Sumayya ta girgiza kai ta ce "A'a, na tsorata da kashedin da aka yi mana, a bar zancen kawai, ban san suwaye mutanen ba". Nabila ta ce "Wallahi sai mun je, akwai wata shashasha da ta isa ta hana ki cigaba a rayuwa, idan ma ba a saka radiyo ba, sai mu kwatsa a media ina da mabiya sosai a social media, sai ayi duk wadda za ayi.!!!" Ayshercool 08081012142 [7/18, 2:10 PM] null: ⚔️*ƘARFE A WUTA ⚔️ *AISHA ADAM (AYSHERCOOL) https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g Page 4 "No Nabila, abun da ki ke yi is too risky, mutanen nan da gaske suke, they mean what they said, kar ki jefamu a matsala" Nabila ta ce"Karatunki ya tashi a banza kenan sumayya? Idonki har da hawaye saboda takaici. Wasu lokutan kin fiye sokwanci sumayya, da ni ce da tuni na ci buhun ubanta". Sumayya ta ce "Ni ce sokuwa ko? na gode amma ni ba zan iya kasadar da ki ke yi ba, na rasa aikina, but wait mu je na rakaki in da aka aike ki mana" Nabila ta ce "Wa? Taɓ tuni na kira MD na bashi uzuri, dama barrister Habib ne ya aike ni, yadda wannan matar ta wurin aikinku take, lawashi ko lotion take, haka yake yi mini, ba ya ƙaunata" "A'a, naki ya sha banban da nawa Nabila, shi taimakonki yake yi ai" Nabila ta kwaɓe fuska ta ce "Ke, idan fa kin ga ina zuƙewa a aikin nan, wanda za a kare ba shi da gaskiya ne, MD zan saka ya canza mini team daga na su Barrister Habib, na Barrister Bashir nake so, wata zazzafar shari'a za su kara, shari'ar manya ce, a kan kuɗi, zuwa zan yi na sha kallo, kuma an ce akwai yiwuwar na haɗu da masoyiyyata kwanan nan" Sunayya ta ce "Wa kenan?" "Anty Naja'atu Bunkure mana, kin san am die hard fan of that woman, Barrister Naja'atu duniya ce, ga gayu malam, harshenta akwai turanci, kamar wadda aka haifa royal palace ɗin Elizabeth" Sumayya ta yi tsaki ta ce "Aikin banza ƴar wahala, ita ta zama abun da ta zama a harkar aiki, har tana burgeki, ke kuma kina zaune kina shashanci, wallahi ƙarshe ki koma ƴar ɗaukar jakarta" Nabila ta ce "Kan uba, degree holder in yi dakon jaka, Kin ci mutuncina fa, Sumayya ta girgiza kai, haryanzu Nabila shirirta da yarinta na damunta. Ko da Nabila ta je gida, tun a tsakar falo take tambayar magajiya, ina DSP. "Bai dawo daga aiki ba, na ji ɗazu yana cewa ko za su je ringin" Nabila ta ce "Aikuwa ya yi ya dawo, sun bayar da maza, in mun zauna ya yi ta cewa police ya fi lawyer, yau zai sha kunya idan ya ji me suka yi. Yau zazzafan debate ne tsakanina da shi, har lemo zan yi mana aji daɗin yin musu" Anty ta ce "Ka ji mashirirciya, musun da za ku yi za ki haɗawa lemo?". "Eh mana, ɗan sanda sharri, lawyer kuma musu" tayi maganar tana dariya. Wani mugun kallo mama ta yi mata, yaran gidan nan har take suke yi wa Nasir da discipline master, saboda yadda suke jin tsoron sa, amma tsakaninsa da Nabila sam ba haka bane ba, suna good time sosai da Nasir, kuma duk gidan bayan Abba ba ta da abokin hira ko shawara sai shi. Nabila ta share mugun kallon da maman ke yi mata, ta tafi ɗaki. Misalin ƙarfe huɗu na yamma, Sumayya ta ga kiran lawisa, kawai ta basar ta cigaba da kallon tv, ta kira ya kai sau huɗu sannan ta ɗaga. "Ki na ji ina kiran waya ki ka ƙi ɗagawa?" "A silent take, bacci nayi ne". "Ki tura mini recodings ɗin nan, su murtala ba su sami wani samo rahotanni masu muhimmanci ba, kuma na ga su Mikiya radiyo duk sun wallafa labarin yaron nan, ki turo mini mu ga wanda za a iya tacewa a saka" Sumayya ta taɓe baki ta ce "To" Ta kashe wayar, ta ce "Allah ya ƙara, da mu muka fara sanar da labarin, kuma mu ka saka a internet, ai da ya fi, tun da ni ce ƴar jarida ta farko da ta fara zuwa wurin, amma ki ka ƙi" Ta lalubo lambar Nabila ta kirata, ta gaya mata abun da ya faru. Nabila ta ce "Amma baki da wayo sumy, ke yanzu sai ki tura mata, saboda ba ki da zuciya?" "To yaya zan yi mata?" "To amma kin san ko kin tura mata, sunanta za ta faɗa a mai rahoton ko wanda ya karanta ba ke ba ko?" Sumayya ta ɗan yi shiru ta ce "Kuma fa haka ne" "To tun wuri ki ce mata kin goge kawai, gobe ba za ta ƙara yi miki wulaƙanci ba". Sunayya ta ce "Haka za ayi, na gode sosai" cikin hanzari ta kira Lawisa, ta sanar mata da cewa ba ta ga recordings ɗin ba. Aikuwa ta hau ta da bala'i, Sumayya ta danna recording tana dariya ƙasa-ƙasa da niyyar ta turawa Nabila. Bayan sun gama wayar, ta turawa Nabila, suka din ga dariya, Nabila na ƙara bata ƙwarin gwiwar, kar ta sake ta ɗauki raini ko wulaƙanci daga wurin lawisa. Ta kuma cigaba da lallaɓa sumayya, a kan lallai ta koma asibiti, ta sake tattaunawa da mutumin nan, ko iya sunan mai laifin ta samo. Barrister Habib ne ya shiga office ɗin MD, ya zauna suka gaisa, cikin takaici Habib ya fara magana, "Barrister, ni fa na gaji da iskanci yarinyar nan, idan a team ɗi na za ta zauna, ta zauna, kuma dole ta yi biyayya ga abun da na sakata, idan wurin Bashir za ta koma, ta koma na gaji da iskanci da rashin mutuncin da take aikatawa, ba ta san aiki ba ko kaɗan" MD ya ce "Calm down Habib, na sani wallahi, na san ku na haƙuri da ita, wallahi nima nauyin mahaifinta nake ji ne, abun da yayi mini a rayuwa idan na kore ta ban yi wa kaina adalci ba, shi ma yana yawan bani haƙuri a kanta, marainiya ce kuma ba ta da cikakkiyar lafiya." "Mu ma duk marayun ne ai, waye yake iskancin da take yi? Ta zo lokacin da ta ga dama ta tafi lokacin da ta so, she's not serious at all" "Na sani, kuma nima ina gani, ka rabu da ita, duk wani abu da za ku yi ku daina sakata a ciki, ƙyaleta da bashir ɗin, shi ne daidai da ita, ku yi haƙuri dan Allah" MD ya din ga lallaɓa Habib, dan ba zai so rasa gogaggen lawyer kamar Habib a law firm ɗin sa ba, a kan Nabila da ba aikin ne a gabanta ba. Yau weekends ne, gaba ɗaya iyalan major na babbn falo, kowa ya ja nasa wuri yana karyawa, Nabila ce kawai babu a wurin. Tun yana jurewa ya kasa, yayi gyaran murya ya ce "Ina arfa ne?" Anty ta ce "Bacci take yi" Ya kalli walida ya ce "Tasota, ta fito ta karya, sai an cinye an bar ta, ta cikawa mutane kunne da kuka" Kusan mintuna goma da taso ta, sannan ta fito, kayan bacci ne a jikinta, dogon wando da rigarsa har gwiwa, kanta babu ɗan kwali. Nasir ya tsura mata ido, ko ƙiftawa ba ya yi. Abba ya ce "Ina kallabinki? Ki ka fito da wannan gashin ba kyan gani, kamar totuwar masara?" Ta saka hular hannunta ta ce "Haba Abba, dan daga bacci na tashi ne fa" "Tafi can ƙazama, kullum kai babu kitso, ba za a rasa kwarkwata a wannan gashin ba" dariya aka hau yi mata. Ko a jikinta, ta zauna kusa da Abba, ta kalli Nasir ta ce "DSP, yaushe ka dawo ba labari, ya hanya?" Ya jinjina kai ya ce "Alhamdilillah" Major da kansa, ya taya Nabila haɗa shayi, ga soyayyen dankali, ga bredin ta, amma tana buɗe bredin ta ce ba za ta ci ba, kwantai ne. Major ya miƙa mata nasa ya ce "Duba zaki iya cin wannan? Dankali kawai ba zai riƙe miki ciki ba" ta duba buredin Abban ta ce "Eh wannan sabo ne, Abba ka ƙara mini ƙwan, ni ba na son dankalin ma" Ya ce "To shikenan, ɗauki nawa da ma ni yanzu ƙwai bai dace da ni ba, a shekaruna" Idan da sabo, sun saba da ganin irin wannan fifikon da major yake nunawa, duk da mutum ne mai ƙaunar yaransa sosai da sosai, amma son da yake yi wa Nabila na musamman ne, amma fa hakan ba ya hana idan suka yi laifi, ya hukunta su kamar ba ƴaƴan cikin sa ba. Anty ta ce "Arfa ba zaki bari Major yayi ƙiba ba, kalli yadda ki ke tara mazaunai, saboda ci" Yayi murmushi ya ce "Tafi kowa girma a gidan nan" Nabila ta ce "Abba, Allah ya ƙara arziki, ka yi ta sayowa mu na ci" "Amin arfan Abba" Nasir ma ya juye mata nasa ƙwan, ta tattare tana dariya, dan ta na son ƙwai sosai. Mama kuwa kamar za ta yi bindiga, saboda baƙin ciki. Bayan an kammala cin abinci, su walida ne suka kwashe kwanukan da aka ci, Nabila kuma ta hau labartawa Nasir, abun da ya faru da sumayya da ta je Asibiti. Fafur Nasir ya ce ƙarya take yi. Ta haɗe rai ta ce "Yaya, wai meyasa a duniya jami'an tsaro ba kwa yadda kun yi laifi, ko wani ne daga cikinku yayi, sai kun ƙaryata, kun kare mutum" "Wa ya gaya miki hukuma tana laifi?" "Ba mutane ne hukunar ba? Ai mutane na laifi, kuma hukuma ma suna yi, wallahi da gaske nake, ka bincika ka ji kuma, koma na kira maka sumayyan" Ya ce "A'a ai ƙarya ki ke yi, ni zaki zauna kawai dan ki ƙure" Duk yadda ta so, ta fahimtar da shi, amma ya ƙi fafur. Abba dai kallonsu kawai yake yi yana dariya, ganin ba zai yarda ba, ya sanya ta ƙyale shi, ta koma wurin Abba. "Abbana" tayi maganar tana ɗan murmushi. Abba ya ce "Kuɗi zaki tambaya kenan?" Ta girgiza kai ta ce "A'a Abba, abu zan tambaye ka" "Ina jin ki" "Abba dama, wata amarya ce, suka kira ni a waya, zan je gida na yi musu make up, ita da ƙannenta na biki, za su biyani, VIP ne har gida" Haɗe rai yayi sosai sannan ya ce "Me na gaya miki a kan wannan sheɗancin? Kin san na hana ki sabgar banzar nan, ban da kalen sheɗanu jikinku, me wannan shashancin zai amafana miki, na fuskanci kin fi fifita wannan kwalliyar a kan aikinki, to babu in da za ki je". "Dan Allah Abba, wallahi zan samu kuɗi fiye da salaryna, dan Allah" "Ba in da zaki, tun da babu abun da ki ka rasa a gidan ubanki, ba matar da zaki bi gida ki na shafawa hoda, idan ta matsu tayi da kanta mana, banda shashanci ace mace ta zauna sai an bita gida shafa mata hoda da gazar" "Abba!" "Shut up" yayi mata tsawa, hakan ya tilasata mata yin shiru. Walida kuwa faɗan Abban dariya ya bata, wai idan sun matsu su yi da kansu, ba wadda za aje gida shafawa hoda. Nabila ta din ga jin ko a ɓoye sai ta je, tana son sana'arta ta kwalliya, Abba kuma ba ya so, wai shashanci ne da fatan aljanu, ita kanta idan tayi a fuskarta wasu lokutan, ya din ga faɗa kenan. Akwai ranar da za ta je biki, ta yi kwalliya ta saka eyelashes, ya kirata dan ya ga meya samu idonta, gashin idonta yayi tsawo haka, tun da ta ce masa sawa tayi, ba ta ankara ba, ya saka hannu, ya fige shi sai da ya haɗa da gashin idonta, ya ce ya kuma ganinta da shi sai ya zaneta. Har a gaban saurayi, ya taɓa korata gida, wai ta je ta wanke fuskarta, ba za ta cuci ɗan mutane ba, duk ta damalmala fuska da hauka, ta zama kamar wata bebin roba. Ta rasa meyasa Abba yake adawa da sana'ar nan tata. Nabila tun a weekend, take cigaba da zuzutawa Sumayya trial ɗin da za su je, kotu ranar laraba, farincikin ta ya kasa ɓoyuwa, wanda hakan ya samo asali ne, da yadda ta ga Barrister Habib ya ƙyale ta, ta koma team ɗin Bashir, kuma ta samu labarin barrister Naja'atu ma tana da shari'a ranar a kotun, dan haka za ta haɗu da ita. Nabila uniform ɗin ta, tamkar su yi magana, saboda ɗaukar guga, ita kanta a bar kallo ce a cikin kayan, ba fara ce tas ba, amma haskenta mai kyau ne da ɗaukar hankali, domin kuwa jikinta kamar ƙwai, dan tana kashewa Jikinta kuɗi ba kaɗan ba, ba ta da wata damuwa, ba abun da take yi da kuɗi, ban da sayen kayan gyaran jiki, ta samu kuɗi a aikinta, major ya bata, Nasir ma ya bata, ga wanda take tatsar samari, ga ƴan sana'ointa, dan haka kuɗi sam ba matsalarta bane ba. Barrister Naja'atu Bunkure matashiyar lawyer, mai dakawa maza gumba a hannu, karo da ita sai lawyern da yake jin kansa ya isa, dan abu ne mawuyaci case ya shiga hannunta ba ta yi wining ba. Ana yawan sanar da ayyukan alkhairin ta, a gidajen rediyo na taimako da tsayawa marasa galihu a kan shario'i daban-daban. Bakin Nabila ya ƙi rufuwa, ganin yau ga ta ga Barrister Naja bunkure, wata ƴar gayu da ita, yadda ta gabatarwa da kotu kanta kawai, ya isa ka tabattar da ta san me take yi, ga yaren nasara a harshenta wato turanci. Gaba ɗaya hankalin Nabila ba ya kan shari'ar, yana kan bunkure, da yadda take magana. Murna kamar nabila ta taka rawa, yau ga ta ga mentor ɗin ta. Sumayya ta samu damar editing news yau da kanta, kasancewar MD yana ta mitar, ta daina ware kanta, ta din ga shiga ana aiki da ita a haka za ta goge. Kiran Nabila ta gani, dan haka ta ɗaga ta ce "Kiran me ki ke yi mini ina aiki?" Sama-sama ta din ga jiyo numfashin Nabila, muryarta ƙasa-ƙasa ta ce "Kin tashi daga aiki ne?" "A'a menene meyafaru?" A galabaice ta ce "Na dawo chamber ne, na ɗauki kayana, ina hanyar komawa gida, ji nake kamar ciwona ne zai tashi, ina titi dan Allah Sumy ki zo" "Subhanallah, gani nan zuwa amma babu wani a wurin da zai kai ki gida?" "Ni ba na son damun kowa, dan Allah besty ki zo, kar na mutu a titi" Ganin ta gama abun da take yi, ya sanya a gurguje ta ɗauki jakarta, ta fita, ba ta tsaya ko ina ba, sai hanyar wurin aikin su Nabila, tana ta rarraba ido a titi tana kiran wayarta. A kan wani tudu ta hango Nabila, idanunta sun yi jawur, da alama tayi kuka sosai da sosai. Ta ce "Mai napep, bari na ɗauketa ka kaimu gadon ƙaya dan Allah, ba ta da lafiya" Ya ce "To shikenan" ta sauka ta rungumo Nabila, ta taimaka mata, ta shiga napep ɗin, sai dai babu baki, sai numfashi take sama-sama. "Arfa, meyafaru an ɓata miki rai ne?" Ta girgiza kai alamar a'a. "To menene? Haka kurum ciwon ya tashi" buɗe baki ta yi, da nufin yi wa sumayya masifar ta ƙyaleta, amma ta ji numfashin ta, zai gudu ya bar huhunta, hakan ya sakata yin shiru. Can kuma a hankali ta ce "Sumayya mu je gidanku, wurin umma" Sumayya ta jinjina mata kai, haka aka yi. umman sumayya na ganinsu hankalinta ya tashi, Nabila ta samu wuri ta kwanta. Umma ta ce "Sumayya, me aka yi mata ne?" "Wallahi umma ban sani ba, kawai kirana ta yi a waya, ciwonta ya tashi" Cikin kuka Nabila ta ce "Umma dan Allah ki yi mini addu'a, ki ƙyale sumayya" Umma ta ce "To shikenan" ta din ga tofa mata addu'a, har aka samu ta yi bacci. Bayan awa ɗaya da rabi, ta farka, har ta samu ta ci abinci ta yi salla, umma ta din ga tambayarta, ko wani abun aka yi mata, amma ta ce a'a. Ganin ta ware, ya sanya umman basu wuri, Sumayya ta sake kallonta ta ce "Ke, wallahi wani abu aka yi miki, yanayinki ya nuna mini, kin ga idonki kuwa, ki gaya mini menene?" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Sumy, ashe haka ake ji, idan aka wulaƙanta mutum mussman a gaban jama'a, a dizaga ka" "Menene? Waye ya wulaƙanta ki?" Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Kin san Naja'atu Bunkure?" "Ba dole na santa ba, a wurinki na santa ai" "Ashe matar nan tsinanniya ce" Da sauri sumayya ta ce "A'uzubillahi, me yayi zafi, mentor ɗin taki?" Nabila ta ce "Zilwajahiani ce, abun da muke ji a kanta daban, yadda take daban. Yau muka haɗu a kotu, kin san ina cikin team ɗin barrister Bashir, tare muka je court yau. Bayan an fito, jiki na tsuma na bita, ƴan jarida sun baibayeta, na yi mata magana kin ga wulaƙantaccen kallon da tayi mini? Ba shi ne ya dame ni ba, duk da uniform ne a jikina, na cire girman kai na gabatar mata da kaina, a matsayin lawyer mai koyi da ita, amma still ban isheta kallon kirki ba. Abunka da zuciya da abun da take so, na matsa tare da miƙa mata wayata, a kan ta bani lambarta, sai ce mini ta yi ba za ta bayar ba, kar na isheta da kira. Na ce mata bakomai, a matsayina na mai koyi da ita, kuma mai ƙaunarta, dan Allah ko mintuna uku ta bani, na daɗe ina burin haɗuwa da ita. Ina son ta bani shawara a matsayina na lawyer mai tasowa, kuma ta bani tips da zan bi, na zama kamarta a rayuwa, dan ina son ta da irin ayyukan da take yi. Ta ƙare mini kallon baki isa ba, sannan ta ce 'Ki zama kamar ni kuma? Taka matsayin da na taka? Never! Don't even give a try, ba zaki taɓa zama ba, and leave my way please, ina da abun yi" Haka fa ta ce mini, a gaban mutane da masu yi mini dariya, da masu yi mini Allah ya ƙara wai neman suna da gidin zama ne ya janyo mini, wasu kuma su ka bani haƙuri wai haka halinta yake. Sumayya yau na tozarta, an wulaƙanta ni, duk yadda nake ganin ina da class, soyayya ta rufe mini ido, saboda ina ƙaunar matar nan fisabilillahi, wallahi da ƙyar na ƙarasa chamber, nan da nan na fara jiri, numfashina ya fara sama, kin ga dariyar da aka yi mini, wallahi na muzanta fiye da tunaninki" Sumayya ta ce "Nabila jikina yayi sanyi, ban taɓa zaton matar nan za ta aikata haka ba, wai meyasa mu mata, galibin mu ƴan baƙin ciki ne? Wato ba zaki zama kamarta ba, sai ka ce wayo da dabararta ne suka ba ta matsayin da take kai". "Wallahi sumayya, ko zan rasa raina, ko da kasada, sai na tabattar da na yi suna nima, sai dai idan Allah ya ƙaddara na mutu. Amma ina roƙon Allah, in sha Allah tana raye, sai na ɗaukaka fiye da tunaninta, kuma bibiyarta zan din ga yi, da bibiyar duk wani abu da ya shafe ta, sai na rama abun da ta yi mini. I will do a background check on her" "Ke fa baki iya ɗaukar abubuwa da sauƙi ba, ki ƙyaleta mana kanta ta yi wa, ni na ce me?, abun da nima ake yi mini, ni kusan kullum ake yi mini, ke yau ne kawai, kuma arfa matsayi na duniya ba na kiyama ba" Nabila ta girgiza kai ta ce "Wannan ke ki ka ga zaki iya, kuma ƙaramar alhaki ce ta wurin aikinku, wannan kuwa dizgin da ta yi mini, in sha Allah rabbi, sai na rama shi, dole na ajiye shirme, na mayar da hankali a kan aikina, ko dan fansar nan, kut wallahi matar nan ta gama cuta ta, kuma ba zan huce ba har sai na rama wallahi. Rakani titi in tafi gida" ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin tashi tsaye. Sumayya ta danƙota ta ce "Nabila ki din ga sanyawa zuciyarki salama mana, kin fiye zafin rai, ki bi komai a hankali, kalli yadda ki ka kusa kashe kanki a banza. Idan Allah ya yi nufin ɗaukakaki fiye da ita, ita ɗin banza ta hana, dan Allah ki manta da ita, ki cigaba da rayuwarki". Ta kalli sumayya cikin takaici ta ce "Lallai ma sumayya, dan ba ki ga abun da ta yi mini ba, a gaban mutane har da masu yi mini dariya. Ni gaba ɗaya ma ji na yi ban yarda da ita ba, abun da ake faɗa a kanta daban, abun da na gani yau a kanta daban, akwai wani abu a ƙasa, and i will run a background check on her, for the first place ma, wacece ita? Idan ta kama har bunkuren zan je mahaifarta, meyasa abun da ake faɗa a kanta daban, ita kuma halinta daban". Sumayya ta ce "Na shiga uku, Nabila" kafin ta yi magana, Nabila ta yi waje, ta tarar da umman sumayya na salla, ta ce Umma na tafi, ta fice daga gidan. Sosai abun da ya faru ya tsayewa Nabila,da ta tuno abun sai wani irin takaici yakamata. Yau ba kowa ya san ma ta koma gida ba, dan yau babu surutu da hayaniya. Abu kamar wasa, har dare Nabila ta kasa walwala, ko fitowa daga ɗaki taƙi yi, gani take kowa yana kallonta zai gane an dizgata yau, duk iyayin na ta da jan ajin. Nabila irin mutanen nan ce masu saka abu a ran su, dan haka ko ta yi niyyar manta abun da ya faru, sai ta kasa. Ta ɗaukko wayarta, ta kunna data, ta tarar da messages ɗin sumayya, ta na ta yi mata faɗan ta yi haƙuri ta manta da abun da ya faru. Nabila ta yi mata reply da "You are not serious, ki saka ido ki yi kallo" Social media ta hau, ta shiga searching ɗin sunan barrister Naja'atu Bunkure, nan da nan sai ga hotunanta, da wasu daga cikin ayyukanta na jin ƙai, sai dai ba ta samu wani cikakken bayani da take son samu a kanta ba. Tsaki ta yi, bayan tuna yadda take mutuwar son matar nan a baya, har hotonta take sakawa a dp ɗin ta, saboda yadda take ƙaunarta, amma lokaci ɗaya a yanzu ji take yi, ba ta da wani maƙiyi idan ba ita ba. Har sha biyu da rabi na dare, ba ta samu cikakken abun da take son sani ba, sai ma zarge-zarge da suka din ga ɗarsuwa a ranta game da matar. Saukkowa ta yi daga kan gadonta, ta fice daga ɗakin, fita tayi can babban falo, ta nufi kitchen ta samu abun da za ta ci, dan yunwa take ji sosai. Fridge ta buɗe, ta samu ruwa mai sanyin gaske, da coc ta fito falo tana sha. Hasken fitila ta hango a baranda, ba a kashe ƙwan wurin ba, ga abba kullum sai yayi magana a kan rashin kashe kayan wuta, kafin a kwanta bacci. Wurin ta nufa, da niyyar ta kashe ƙwan, ta na zuwa ta leƙa, ta hango nasir a kan kujera, yana ta danna system. Ta window ta je ta zura hannu, tana taɓa masa kunne. Caraf! Ya riƙe hannun ba tare da ya ɗago ba. Tayi dariya ta ce "Shi ne ba ka tsorata ba" "Me ki ke tunanin zai razana ɗan sanda?" Ta ce "Ai dai ɗan sanda mutum ne, kuma na san ka ji tsoro mazewa ka yi" Yayi murmushi ya ce "Tsoro sai lauyoyi" Ta buɗe ƙofa ta fita ta zagaya in da yake ta ja kujera ta zauna sannan ta ce "Duk tsoron lauya bai kai ɗan sanda ba" Ya ɗago ya kalleta, sanye cikin kayan bacci pink, masu bargo kanta ko ɗan kwali babu, tayi parking ɗin gashinta" Murmusawa yayi ya ce "Ke kin san babu tsoro ga wanda yake riƙe makami, yayi yaƙi da ɓarna" "Hmm, yi dai a hankali, dan harshe ya fi makami dafi, kar lauyoyi su baka mamaki watarana" "Ina aiki kin zo zaki dame ni, ina nawa aikin, ina kallabinki?" "Yana ɗaki" tayi maganar tana lashe murfin jarkar lemon hannunta. "Kalli abun da ki ke yi kamar ƴar ƙauye, sai an yi magana ki fara ke barrister ce, ke degree holder " yayi maganar yana mayar da hankali a kan system. Ta numfasa ta ce "Wai aikin me ka ke yi ne?" "Wani aiki ne mai wahala, wanda nasara a kansa, na iya sawa na samu cigaba a aikina". Nabila ta ce "Haba dai, to Allah ya taimaka" "Amin" ya amsa ba tare da ya kalleta ba. Shiri ya wanzu na wani ɗan lokaci, sannan ta ce "DSP" "Na'am barrister" "Sannu da aiki" ya ɗago ya kalleta ya ce "Kin isheni fa, za ki tashi ki bar wurin nan" "Yi haƙuri, na daina magana" Ya cigaba da aikinsa, ta na shan lemonta, tana jin yadda iska ke kaɗata. Duk abun nan, Abba ta ɗakinsa ya na hango su, sai dai ba ya jin me suke cewa. Can ta sake cewa "DSP" A hasale ya ce "Ke! Meye ne? Tashi ki je ki kwanta dare yayi" "Ni na kasa bacci, raina ne a ɓace". "Ai dama kullum cikin ɓacin rai ki ke, tun da ke a rayuwarki ta duniya, baki da haƙuri tashi ki bani wuri" Ta marairaice ta ce "To ka tsaya ka ji me aka yi mini mana, dan Allah kafin na tafi, ka gaya mini me zan yi, wanda zai saka na yi suna, kowa ya sanni" tayi maganar very serious. Cikin gatse ya ce "Ki nemo in da Aminu Viper yake, ki taimaka mini na kama shi, kin ga sai ki yi suna, ni na samu cigaba a aiki" Ta fuskance shi sosai ta ce "Waye shi, a ina yake? Kamar na taɓa jin sunansa" Ya kalleta ya ce "Shi nake ta aiki a kansa, galibin aikin ta'addancin da ƴan daba suke yi, a wasu shiyyoyin da saka hannunsa, yaransa ne. An ce lallai na kamo shi, tun da yankin da ake ɓarnar ƙarƙashin kulawata yake akwai zarge-zarge a kan guduwa yayi daga prison" "Dan Allah idan na nemo maka shi, zan yi suna, kowa ya sanni?" Kallon baki da hankali yayi mata, ya cigaba da abun da yake yi. "Ka ga riba biyu kenan, na yi suna, kuma ka samu cigaba a wurin aiki, yes! Amma na ji ka ce akwai zarge-zarge a kan guduwa yayi daga prison how? Kun tabattar da hakan ko kuwa? Ka bani hints mana, laifin me ya yi a ka kai shi prison ɗin?". Takalminsa ya ɗauka ya miƙe tsaye ya ce "Tashi ki bar wurin nan, tashi maza" Da haka ya koreta, ta tafi ɗakinsu. Sai dai  da ga koma ɗakinta, ta dinga sintiri a cikin ɗakin, sosai ta ji maganar Yaya Nasir ta shiga ranta, ina ma hakan ta tabatta. "In taimaka masa ya kama ɗan ta'adda, in nemo haƙiƙanin dalilin barinsa daga gidan yari, idan guduwa yayi me ma'aikatan suke yi, idan sakinsa aka yi laifin me yayi, aka sake shi duk da hatsarinsa, na bankaɗo ainihin identity ɗin Naja'atu Bunkure, na gyara career ta, wai ma menene dalilin da ya sa ban zama ƴar sanda ba?, na zama wata lauya yau ka kare mai gaskiya gobe mara gaskiya. Ta yi wani irin shu'umin murmushi ta ce "Accepted DSP Nasir, zan nemo maka Aminu Viper, na bibiyi laifin da ya aikata, da yadda aka yi ya bar prison. Ayshercool. 08081012143 [7/19, 1:11 PM] null:                                     *ƘARFE A WUTA* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION BRIGHT PENS SECOND BATCH. https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g 5 Wurin shiru, ba ka jin motsin komai, hantsi yayi, yana zaune a kan wani dutse, yana jin yadda ɗumin ranar ke ratsa shi, dan ba ta riga ta yi zafi ba, hannunsa ɗaya ɗauke da taba sigari, yana ta zuƙa yana busawa, idonsa yayi jawur. "Viper" matashin  ya kira sunansa, yana ta sauke haki. "Ina jinka" yayi maganar ba tare da waiwayawa, ya kalli matashin ba. "An kama ɗan mama da kayanmu fa jiya da daddare, a chamber yamma da gari, yana tsaka da raba kayan ga mutane, kuma wadda aka kama da yawa" Ya saka yatsansa ya ɗan daki jikin sigarin, tokar jiki ta zube, ya ja numfashi ya ce "Wace hukumar ce?" "Masu ƙwaya ne" Ya miƙe tsaye ya ce "Shikenan, kar ka damu, ku bar shi a hannunsu" Ya waro ido ya ce "A bar shi, Ka manta a halin da ake ciki? Idan wani abu ya faru fa?" Cikin takunsa na ƙaƙƙarfan namiji, ya ƙarasa gaban matashin, ya riƙe kwalarsa a hankali sannan ya ce "Ba na butulci walid, ɗan mama ni yake yi wa aiki, dole na fito da shi. Ni ba zan kamu ba, da zan kamu da basu bari na fito ba. Kuma ko a yanzu suna sane suka bar guzuma, suke harbin karsana. Ni na shirya a kama shi, sannan ina son ku je dabar Madaki, ko wurin da yaransa suke, ku tayar da hayaniya, ku zubar da jini, kar ku raga musu ko kaɗan, ko da kuwa hakan yana nufin jami'an tsaro su kama ku" Yayi shiru yana kallon viper. Ya shafi sumar walid, da tayi cibiri-cibiri ya ce "Ya ka ke kallona kamar kana tantama a kaina?" Ya risuna ya ce "Tuba nake mai gida, duk abun da ka ce dole ayi shi, umarninka muke yi wa biyayya" "Good. Idan aka kama ku, ko da mutum ɗaya ne daga cikinku, ku ambaci sunana, ku ce ni ku ke yi wa aiki, ni ne na saka ku. Ina sake jaddada maka, kar ku ragawa kowa a cikin su. Amma ku kiyaye ƙa'idar aikina. Babu kisan kai, babu taɓa wanda babu ruwansa mata ko kuma ƙanan yara" Walid ya ce "An gama maigida" " Ɓace " ya furta a hankali. Yau Nabila ko karyawa ba ta tsaya yi ba, haka zalika ko sumayya ba ta jira ba, ta tafi aiki. Daga office ɗin ta, tana hangen harabar chamber, ta ga isowar motar Barrister Bashir. Bayan mintuna talatin ta bishi office ɗin sa, suka gaisa ya dube ta ya ce "Ƴar ƙwalisa ya jiki?" Ta ce "Jiki kuma, ba ni da lafiya ne?" Ya ce "Ranar da muka dawo daga court, kina ta tari har ki ka tafi gida, ko kin manta?" Ta ce "A'a na tuna, na ji sauƙi ai" "Wai meyafaru ne a kotun, bayan na je na ga abokina, da na dawo na tarar da ke gaba ɗaya ranki a ɓace, na tambayeki kin ce ba komai" Nabila ta ce "Da ma fa dan bana jin daɗi ne, ai ni ba zan manta da ranar ba, na ga masoyiyata kuma mudubina" Barrister ya ce "Wa kenan?" "Barrister Naja'atu, ina son matar nan sosai " Yayi murmushi ya ce "Bunkure ki ke nufi?, mace mai hatsari kenan" Ta waro ido ta ce "Hatsari kamar yaya?" "No, kin san ba ta da wasa da aiki, duk shari'ar da ta saka gaba, sai ta ga bayanta, ke kuma gashi ba haka ki ke ba, ba kya mayar da hankali a kan aikin". "Ai in gaya maka ganinta kawai da na yi, na ji wata irin ƙwarin gwiwa, na ji sonake na nutsu na mayar da hankali sosai a kan aikina. Sonake na bi footsteps ɗin ta, nima na yi nasara kamar ita. Amma me ka sani a kanta da zaka iya gaya mini?" Yayi murmushi ya ce "Nothing much, ki tambayi barrister Habib, ya santa sosai " sai da ta ji wani dummm! Yadda suke faɗa da barrister Habib, amma hausawa su ka ce ranar biyan buƙata, rai ba a bakin komai yake ba, dan haka ta ce "To shikenan, na gode sosai ayi aiki lafiya". Ta juya ta fita tana nanata "Dangerous woman, zamu gani ai". Ba ta zame ko ina ba, sai ofishin barrister Habib, ta tarar da shi da wasu client suna tattaunawa, ya ɗago ya kalleta ya ce "Meye?" A ɗan hasale dan a ƙule yake da ita. Ba tare da ta yi fushi ba, ta yi masa murmushi sannan ta ce "Wurinka na zo, amma bari na jira ka gama". "Idan na gama ina da abun yi" ya faɗa a taƙaice. "Dan Allah yaya habib ko mintuna goma ne" "Na gaya miki ina da abun yi, fita ki bani wuri" tsayawa ta yi tana kallonsa, tare da tura baki, babu alamar ma za ta fita ɗin. "Ba magana nake yi ba?" A shagwaɓe ta ce "Dan Allah" Ɗaya daga client ɗin ya ce "Barrister a taimaka mana, kar ta yi kuka" Ya ce "Ta daɗe ba ta yi ba, ba zaki fita ba?" Nabila ta ce "Ya ka ke korata kamar wata kare ne? Na san ina yin laifi, ka yi haƙuri na shiryu ai" Tsaki yayi, ya cigaba da rubuce-rubuce. Ta tura baki ta fice, a zuciyarta ta ce "Ai ko da me ka ke yawo, sai na samu abun da nake son ji a wurinka" Ta je ta samu MD, suka gaisa, sannan ta ce "MD, ka ga Barrister Habib ko, na je na bashi haƙuri, amma ya kore ni a gaban mutane". Ya yi murmushi ya gyara gilashin fuskarsa ya ce "Anya ba wani laifin ki ka yi masa ba?" "Ba laifi na yi masa ba, haƙuri na je ba shi fa, amma ya kore ni a gaban mutane" MD yayi murmushi ya ce "Ai ke ɗin ce ba kya ji, ya so ya koya miki aiki yadda yakamata, mussman yadda ki ke da faran-faran da mutane, amma ki ka ƙi ba kya so, idan ya saka ki aiki ki ƙi yi, dole ku din ga faɗa ai" Nabila ta ce "Na daina fa, so nake na zama ƙwararriya a kan aikina, ko dan farincikin Abbana, ku yi haƙuri" Ya jinjina kai ya ce "Shikenan, Allah ya sa, ki je ki bashi haƙuri" Ya ce "Bayan ya kore ni, yauwwa sir dan Allah ka san barrister Naja'atu Bunkure?" Ya jinjina kai ya ce "Yes, she's famous a tsakanin lauyoyi, har ma da jama'ar gari ma, ai sananniya ce sosai" Nabila ta yi murmushi ta ce "Wow ina yin matar nan sosai da sosai, yadda take gudanar da aikinta, ya ƙara jan hankalina a kan aiki, ai mun ganta kotu a lokacin da mu ka je kotu last, ni da barrister Bashir, ƴar gayu da ita" "Nabila, ke dai ki na son harkar gayu, amma ba gayun ba, ki mayar da hankali sosai a kan aiki, ki yi ƙoƙari ki kamo ta, ko ma ki fi ta". "In sha Allah, na yi maka wannan alƙawarin but i need your support" Ya murmusa ya ce "Kin samu, ɗari bisa ɗari, ƴar gidan major" "Yauwwa to ka bawa barrister Habib haƙuri, zan koma team ɗin sa dan Allah kar ya sake korata, mussaman a gaban mutane" "To za a bashi in sha Allah" Ta miƙe tsaye tare da faɗin "Godiya nake" ta fice ta bar office ɗin cikin nishaɗi. "Bunkure na ki zai zo mini da sauƙi, saura kuma Aminu Viper" *** Major ya ɗan tsurawa Uwargidan sa mama da ta tattare kwanukan da ya kammala cin abinci. Ta ɗago su ka haɗa ido, ta ce "Ya dai?" "Nasir" "Me yayi?" "Ki ja masa kunne, hawainiyarsa ta kiyayi ramata, na daɗe da gane in da ya dosa, amma tun da kin daƙile abun, to ya ƙara nesanta kansa da ƴa ta, kar ya kuskura in ji ko in ga wani abu da zai sosa zuciyata, kuma kar ya kuskura ya saka ta fara son shi, tun da ba ki amince ba, balle a jefa ta cikin yanayi mara daɗi". Cikin rashin fahimta ta ce "Amma major, wani abun ya yi ne?" "Bai yi komai ba,gugar zana dai nake yi, idan ma yana shirin yin, to ya shiga hankalinsa" cikin mamaki take bin sa da kallo, tabbas idan aka ji major  yana magana da kurman baƙi, akwai abun da ya gani, kuma ko me za ayi, ba zai fito yayi bayanin abun da yake nufi ɗin ba. **** Kamar ɓarawo haka yake zagaye tilon matsakaicin gidan, wanda can nesa da gidan, kamfanunnunka ne, sai gonaki. Cikin ƙasaita yake tafiyar, yana yi yana duba ƙaramar wayarsa mai madannai. Kamar korarre, haka wani matashi ya ƙaraso in da yake tsaye. Ya ɗaga kai ya kalle shi ya ce "Menene labari, yaya aka yi ka fito?" Cak matashin ya tsaya, ya ce "Wai dama ba kai ne ka fito da ni ba?" "Me zan tambaya idan na san komai?" Yayi maganar a ɗan hasale. "Wallahi master.... Cikin wata irin razananiyar tsawa ya ce "Kar ka sake kirana da wannan sunan" Cikin tsuma ya ce "Tuba nake oga, suɓutar baki ce, ban san waye ya fito da ni ba, kawai cewa aka yi na tafi" Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Kuma ka tabattar da ka gaya musu sunana, cewar ni ne me kayan?" "Wallahi na faɗa musu" Ya jinjina kai ya ce "Shikenan" Ya ɗaga rigarsa ya zaro wata sharɓeɓiyar wuƙa, ya danƙa masa ya ce "Maza ka fasa cikin gari, unguwarmu, su walid sun tafi yaran Madaki zaku farwa babu sani babu sabo, idan an yi ram da wani daga cikin ku, ku ambaci sunana, ku ce ni ne jagoran aika-aikar, amma ku kiyaye ƙa'idar aikina" Ɗan mama ya risuna ya ce "Umarninka ne abun biyayya a gare ni, an gama za ayi yadda ka ce" ya soke wuƙar ya juya, ya tafi da sauri yana haɗa hanya.. Cikin ƙaramin gidan ya shiga, ya nufi ɗakin kwanansa, ya kunna fitilar wayarsa, ya kunna ƙwan solar, haske ya gauraye ɗakin. Ya saka mukulli ya rufe ɗakin, sannan ya zauna yayi shiru tsawon mintuna, daga bisani kuma ya ɗaukko wiwi ya naɗa ta, ya kunna ya fara zuƙa. Madadin ya ji ƙunci, da zafin da zuciyarsa ke yi masa, yana raguwa, sai ma wani irin baƙin ciki da matsananciyar damuwa da suka kawo masa ziyara. Wani abu mai tsananin ɗaci yake ƙoƙarin haɗiyewa, amma abu ya gagara. Ya ɗaga wiwin yana kallonta cike da baƙin ciki da takaici, yayi watsi da ita yana sauke numfashi. Kamar mahaukaci ya zabura ya buɗe wata akwati, ya ɗaukko kwalaben allura, ya farfasa ya haɗa, ya yi wa kansa, ya nemi wuri ya kwanta. Bai fi mintuna goma ba, kansa ya fara barazanar tsagewa, ya fara kakari yana rirriƙe kansa. Duk yadda ya kai ga ƙara yawan doses ɗin abun da yake sha, ba sa ɗaukarsa, su mantar da shi damuwarsa, sai dai su wahalar da shi, shi a yanzu babban fatansa ya samu abun da zai yi amfani da shi, da zai goge masa komai  na ƙwaƙwalwarsa ya yi bacci mai nisan gaske. *** Nabila ce tsaye a kitchen tana ta ciye-ciye, tana yi wa magajiya surutu. Baba magajiya ta ce "Dan Allah Arfa ki yi mini shiru na ji radiyona, wai ni ya aka yi, ki ka tashi da sassafen nan ma" Nabila ta yi murmushi ta ce "Baba magajiya kin gane mai muryar nan kuwa?" Baba magajiya ta yi dariya ta ce "Sumayya ce mana" "Ashe za ki gane ta" "Ka ji ƴa, yau na sanku da ke da ita, da zan kasa gane muryarta" "Ai in gaya miki baba magajiya, wata mata ce ta takura wa aminiyata, a wurin aiki, da iskanci kala-kala ga sumayya da son aiki, amma matar nan tayi ta taɗiyeta, ni kuwa na ce ta daina saurara mata wallahi,shi ne ma fa ake ba ta karanta rahotanni wasu lokutan, da experience ɗin ta da komai, wata sokuwa ta cuceta, ta hana ta cigaba" Baba magajiya ta ce "Ohh Arfa, ai mahaƙurci mawadaci, yawan faɗa ba shi da amfani" Nabila ta ce "A'a fa baba magajiya, ni ma ba faɗa ne da ni ba, wulaƙanci ne ba na so, duk wanda ya wulaƙanta ni, sai mun yi fito na fito da shi". Baba magajiya ta ce "A dai din ga haƙuri, tun da.... ba ta gama magana ba, Nabila ta yi wani irin tsalle ta ɗauki radiyon, tayi waje da gudu. Sashin mama ta faɗa, dan ta san tun da Nasir yana gari, lallai zai shiga sashen ta ya karya kafin ya fita. Aikuwa a sashen ta tarar da shi, yana karyawa, su na hira da mama, da kuma sauda. Ƙaro volume ɗin radiyon tayi, ta na yi masa nuni da ya saurara. Rahoto ne a kan rikicin faɗan daba, da ya gudana a cikin ɗaya daga manyan unguwannin kano, wanda tun goma na dare ake rikicin, har ƙarfe sha biyu ana rigimar, ƴan sandan sun yi nasarar cafke wasu daga cikin matasan, in da ɗaya daga wanda aka kama, ya ce Aminu Viper ne ya aka su Sai da suka kammala ji, Nabila cikin rawar jiki ta ce "Yaya Nasir, ba wannan ne wanda ka ke nema ba?" Ya jinjina mata kai ya ce "Shi ne" "Ka yi sauri ka tashi, ka je division ɗin da aka tsare ƴan daban, a baka su ka zurafafa bincike, gidan radiyon su sumayya ne, sai na biya can na sake samo rahoto". "Ke!" Mama ta daka mata tsawa, har sai da ta ɗan razana. "Tashi ki bani wuri, yaya ina magana da shi, ba sallama ba gaisuwa babu neman izini, kawai ki zauna ki na surutun banza" Nabila ta yi shiru ba ta ce komai ba. Sauda ta ce "Dama mama yaushe za ta gaishe ki, tana abu kamar mahaukaciya" Ta kalle su, ta kalli Nasir da yake wurin, ta haɗiye wani abu ta tashi, za ta fita. Nasir ya riƙo hannun ta ya tashi ya tsaya, ya ce "Sorry barrister, na gode sosai da wannan gudunmawa, zan je division ɗin, ki samo mini bayani a wurin sumayyan". Ya kalli mama ya ce "Haba mama, kin san tana gaishe ki, tsananin zumuɗin ta kawo mini labari ne fa ya sa ta manta, thank you Arfa ki shirya ki tafi aiki kar ki makara" A ƙule mama ta ce "Wai kai har abada ba zaka yi hankali ba, dan ubanka ya zauna yana cewa in ja maka kunne, a kan shishshigin da ka ke yi mata, amma ina magana kana dizagani a gabanta" Nabila ta yi gaba ta fice a fusace, dan idan ta cigaba da tsayuwa, za ta iya aikata abun da zai hana kowa wuni cikin farin ciki. Ya ce "Ni ɗin kuma mama?" "Kai ɗin fa, ko ka shiga hankalinka, ko kuma duk abun da ya biyo baya kai ka so". Sam sai ya ji maganar kamar maman ce, ta shirya kayarta dan ta saba, dan haka ya yi musu sallama ya fice. A gurguje ta tsaya ta gaisa da Abba, ta fice cikin zumuɗi, gidan radiyon su sumayya ta fara tsayawa. Sumayya ta yi mamakin ganinta, ta ce "Hajiya lafiya ki ka zo mana wurin aiki da sassafe? Talla ki ka kawo ko cigaya?" "Ƙaniyarki na kawo" Nabila ta ba ta amsa. Sumayya ta ce "Ai na san ke ungulu ce, ba kya jewar banza, ya aka yi uwar makara" Nabila ta ce "Yau da safe kan na fito, na ji baba magajiya na jin program ɗin ku na labaran ƙarfe shida, bayan kin karanto  naki, na ji wani rahoto na faɗan ƴan daba, jiya a kano" Sumayya ta ce "Eh meyafaru?" "Kin je wurin ne?" Sumayya ta zaro ido ta ce "In je in yi me?" "Na ji an ce wai yaran Aminu Viper ne" Sumayya ta ce "Eh to, ni ma haka na ji" "Dan Allah ki tashi mu je asibiti, an ce an kama wasu, wasu kuma da aka yi musu miyagun raunuka suna asibitin koyarwa na cikin gari" Sumayya ta ce "To wai ke duk menene haɗinki da hakan?" Kamar Nabila za ta yi kuka ta ce "Sumy ban gaya miki ba? Yaya Nasir ne incharge ɗin bincike a kan mutumin nan, kusan kullum sai an faɗi mugun aikinsa, ya tabattar mini da in dai na gano masa in da yake, ko na taimakasa ya gano zan yi suna sosai" Cikin matsanancin takaici Sumayya ta ce "Tashi ki tafi ko na ɗura miki ashar, ƴar wahala, shi yaya Nasir ɗin ne ya gaya miki haka? Ƴar sanda ce ke? Su ma ya suka ƙarke da su balle ke ki na mace, wallahi ba zan kai kaina ga halaka ba" "Sumy ki gane, this can all help our career ki zo mu je mana" "Wallahi ba zan shiga shirgin ƴan daba su kashe ni ba, idan kin yi sunan uban me zai ƙara miki, za a binneki da shaharar ne idan kin mutu?" Cikin ƙoƙarin son fahimtar da sumayya ta ce "Ba za a binne ni da shahara ba, amma atleast zan samu chances da zan iya fuskantar Naja bunkure" Wata uwar ashar sumayya ta yi wa Nabila, ta tashi ta ce "Mahaukaciya, ai sai ki yi, ke da bunkuren ƴan wahala" Nabila ta tashi a fusace, ta ɗauki jakarta ba tare da ta sake cewa sumayya komai ba, ta tashi. Sumayya ta girgiza kai ta ce "Arfa Allah ya taro ki ya shirye ki, ya yaye miki baƙin taurin kai" "Tun da kin ce ba zaki je ba, kar ki sake yi mini magana, kuma na gode" "Eh ba zani ba, haka kurum a kashe ni a banza, mutanen da ba tsoron Allah ne da su ba, mutanen da suke shan ƙwaya tana gaya musu gaibu, su ɓantarani biyu a banza ba da ni ba" Nabila ta yi mata shiru ta fice. Nabila ba ta yi tunanin komai ba, ta garzaya asibitin koyarwa, na cikin gari. Ba ta wani sha wahala ba, saboda tana zuwa, ta tarar jami'an tsaro sun kewaye sashen emergency, ba wanda yake shiga ko ya fita. Zagaye harabar wurin ta fara yi,tana neman hanyar shiga, da son tabattar da abun da yake faruwa a wurin, ta samu wata cleaner, ko meyafaru a in da ƴan sandan suke. Nan ta sanar mata da cewa, yaran da aka illata a wurin faɗan daba a daren jiya, aka kawo an hana kowa shiga ko fita. Nabila ta yi mata godiya, ta yi mata alheri, ta nufi wurin da aka hana shigar da fita.. Ta ƙarasa ta samu ɗaya daga cikin jami'an tsaro suka gaisa, sannan ta nemi shiga, suka ce ba za ta shiga ba. ID card ta nuna musu, amma ɗaya daga cikin su ya ce "Madam nan ba prison bane, kuma ba police station ba ne ba, nan Asibiti ne, ki bari idan aka kai su can, sai ki je ki yi aikin ki". Ta kwantar da murya ta ce "Dan Allah yallaɓai, ku bar ni na shiga, Ma'aikaciya ce nima" "Get out from here" yayi mata tsawa. Aikuwa ta hasala ta ce "A beg, don't shout at me, aikinka ka ke yi, nima nawa nake son yi, a kan me za ka yi mini tsawa?" Hankalin mutane ya fara dawowa wurin. Sake hayayyaƙowa Nabila yayi, amma cikin dakiya da taurin kai, take mayar masa da martani. Da ƙyar aka rarrashi police ɗin, dan cewa yayi sai sun tafi da ita station, wataƙila ma ƴar ƙunar baƙin wake ce, ko ta na da alaƙa da masu laifin. Nabila ta ce "Ni za ka yi wa sharri, ki in ƙunar baƙin waken zan kai, zan tsaya saurarku ne, da yanzu wani zancen ake ba wannan ba". Ana ta ƙoƙarin sasanta magana, amma Nabila ta ƙi yin shiru. Ta ciro wayarta, ta kira Nasir sai huci take yi. Yana ɗagawa ta ce "Yaya, ya ake ciki ne? Akwai wani labari ne?" Ya ce "No, wallahi arfa kin ganni, na zagaya station uku a yankin, duk ba a kai su ba, amma wata majiya ta tabattar mini da sakinsu aka yi, just recently" "Sakin su kuma? Saboda me?" "Ban sani ba, a kan abun da nake ƙoƙarin yin bincike kenan" "Ka hanzarta ka taho asibitin cikin gari, akwai waɗanda aka kwantar, police sun hana shiga sun hana fita, an hana kowa shiga, ko da kuwa kusa da ɗakin. Har da ƴan jarida ma an hana su" Cikin sauri ya ce "Ok shikenan, gani nan in sha Allah, hankalina bai kai kan in zo asibiti ba ma na duba ko akwai abun da zai taimaka mini, amma gani nan stay safe" Ta amsa da "Ok" Ta ajiye Wayar a jakarta, ta cigaba da kaiwa tana komowa, ƴan sandan suka saka mata ido, dan kar ta yi wani mummunan yinƙuri, dan ba su san manufarta na dagewa a kan son shiga wurin ba. Babu tsammanni aka fito da matasan, wasu ɗauke da raunuka, wanda ba za su iya tafiya ba, an turo su a kan gado, an nufi hanyar barin emergency da su. Nabila ta nufe su cikin sauri, amma ƴan sanda suka tare ta. Ta kalli ɗaya ta ce "Yallaɓai ina za a kai su? Na ga wasu a mugun yanayi, ya za a bar asibiti da su?" Babu wanda ya kula Nabila, aka saka matasan a cikin ambulance, har da iyayen wasu daga cikin matasan jami'an tsaron suka hana su bin su, suka rufe ambulance ɗin, su kuma su ka hau ta su motar ta ƴan sanda, suka bar harabar asibitin. Ƴan jaridar da suka yi ƙoƙarin bin su ma, aka dakatar da su, aka hana su ƙarasawa ma in da motar take har suka tafi. Tsayawa ta yi kamar wata shashasha, tana mamakin yadda abubuwa suke tafiya, kamar a film. Motar DSP Nasir ce ta shigo cikin harabar asibitin, yayi parking ya fito, yana ƙoƙarin kiran Nabila a waya,ya tambayi tana ina. Da sauri ta ƙarasa in da yake, tana kallonsa, amma ta kasa magana. Ya ce "Yaya dai? A wane ɓangaren suke, kin samu ganin na su kuwa?" Nan ta kwashe duk abun da ya faru, ta gaya masa. Cikin asibitin ya shiga, tana biye da shi, ya tambayi office ɗin incharge na A&E ɗin, ya gabatar masa da kansa, tare da yi masa tambayoyi, a kan dalilin da ya sa, aka sallami mutane da raunuka a jikinsu. Amma ya tabbattar masa da cewa, babu wanda yayi musu wani cikakken bayani, kawai ƴan sanda sun kawo musu yaran jina-jina tun a daren jiya, sun ba su kulawar da ta dace, daga bisani ƴan sandan suka ce asibiti za su canza musu, aka tafi da su. Nabila ta yi shiru, sannan ta ce "Akwai wata a ƙasa yaya Nasir, ko waye wannan Aminun, ya na da wanda su ke sponsiring ɗin sa. Shi an kasa kama shi, amma ya na saka yaran mutane ta'addanci, you need to put more effort, and i will hundred percent support you, everyone is equal before the law, dole a nemo shi a hukunta shi" Ayshercool 08081012143 [7/20, 2:02 PM] null: *ƘARFE A WUTA* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g. 6 Nasir ya ce "Sannu da ƙoƙari arfanmu, amma ki daina saka kanki a risk kin ji ko? Zan cigaba da ƙoƙarina in sha Allah sai na yi sanadin kawo ƙarshen ta'addanci da harkar daba a garin nan, domin kuwa yana ci mini tuwo a ƙwarya nima, but for now mu je na kai ki wurin aikinki" Nabila ta ce "DSP, dan Allah idan ka gano wani abu na rashin gaskiya, ko waye yake da hannu a ciki, ka tona masa asiri. Dan ina ga sumy zan yi wa magana, su faɗi abun da ya faru a gidan rediyo, an saki waɗanda aka kama, kuma wanda aka ji wa rauni ma, an hana kowa zuwa wurinsu, daga bisani kuma jami'an tsaro sun kwashe su daga asibiti, babu wanda ya san in da aka kai su, wannan wane irin abu ne?" tayi maganar cikin haƙiƙancewa. Yayi murmushi ya ce "Kar ki soma, ki na wasa da hukuma arfa, yanzu sai ki kwana a ciki ke, yanzu dai mu je mota" haka ya tasa ta a gaba zuwa mota, suna tafe tana mita. "Wallahi yaya na fara sarewa da lamarin ƙasar nan, anya kuwa gyaran ake so ayi da gaske, ta yaya za ace an gagara kama mutum ɗaya? Ana yekuwar ana nemansa, amma kuma ana kare laifukan da yake aikatawa, ni na kasa gane kan wannan lamarin. Ni fa muddin na gano wani abu na rashin gaskiya, sai na yi magana" "No Arfa, ba huruminki bane ba, ba kuma aikinki ba ne ba, kar ki kuskura ki saka kanki a hatsari, ƴa mace ce ke lamarin ƙasar nan ya wuce tunaninki, ba abu ne mai sauƙi kamar yadda ki ke hangensa ba" Ta yi ajiyar zuciya, sannan ta ce "Yaya garin nan yana kan gaba a garuruwan da ake ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, duk al'ummar da matasanta suka lalace da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi ba ta da gobe mai kyau, matasanmu su ne tushen al'umma mai kyau" Nasir ya ce "Na fuskanci abun da ki ke nufi, but is still not your field" Tayi shiru ta mayar da hankalinta kan titi, tana ta tufka da warwara a zuciyarta. Ko da ya kai ta wurin aiki, ta sauka suka yi sallama, ta shiga tana shiga office ɗin ta, sumayya ta fara kira. Sumayya ta ɗaga ta ce "Kin gama fushin ne?" "Ke ware ba wannan ba, matsoraciya da ba ki je ba ni na je, na samo labari, ina ga bayyana labarin ka iya janyo hankalin manya a cikin lamarin" Sumayy ta gyara zama ta ce "Labarin me?" Nabila ta gaya mata komai, yadda yaran da aka kama suka yi ɓatan dabo, da yadda aka fice da na asibiti ba tare da sanin ina aka kai su ba. Sumayya ta ce "Nabila lallai wannan magana ce babba, bari zan yi magana da MD na ji mai zai ce, gaskiya yakamata a zurfafa bincike a kan lamarin nan". Cikin zaƙuwa ta ce "Dan Allah sumayya ki ƙoƙarta, ayi a sanar, a ji mai hukuma za ta ce a kan haka, ko kin san shi kansa Aminu Viper ana zargin ko dai guduwa yayi daga gidan yari, ko kuma sakinsa aka yi ba bisa ƙa'ida ba, shiyasa ake tsananta nemansa yanzu" "Ke ya aka yi ki ka sani?" "Yaya ne ya gaya mini, akwai lauje cikin naɗi a lamuran mutumin, mutum kamar wani sheɗani". Sumayya ta yi shiru sannan ta ce "Bari, yadda mu ka yi da su zan gaya miki, amma maganar nan ta ɗauki hankalina sosai" "To shikenan, ina saurarenki, yadda ake ciki, ki sanar mini" suka yi sallama. Haka kurum zuciyar Nabila ta cigaba da azalzalar ta a kan lallai tana son sanin wanene wannan Aminun, akwai yiwuwar ta samu gagarumar nasara idan aka ce da saka hannunta wurin kama shi, shahararta ita zai ba ta damar yin gaba da gaba da Naja'atu Bunkure. Sai kuma ta tambayi kanta, for the first place, laifin me ya yi aka kai shi prison, har ake tunanin ya fita ba bisa ƙa'ida ba?. "Akwai ayar tambaya a kan abubuwa da dama" ta yi maganar a fili. *** Ƙurawa wayar gabansa ido yayi, yadda take ta vibration kamar ta tashi, a wannan karon ma private number ce, lambar da ko ta halin ƙaƙa yake fatan ganin ko waye mai ita ya bayyana a gare shi. Ɗan mama da ke kusa da shi ne, ya ɗaga wayar ya sanyata a hansfree, ya tura masa gaban sa. Daga cikin wayar aka ce "Manya gatan wasa, ko ka  tsorata ne ya sanya ka gagara ɗaukar wayata?" Yayi shiru bai ce komai ba. "Idan za ka kwana dubu kana ɓarna, zan kwana dubu ina goge ta, ina ɓatar da sahunka. Ka na ta cigaba da aikata ɓarna, saboda kana son lallai sai ka san waye ni ko?" "Wanene kai?" Yayi maganar a ɗan hasale. Mutumin yayi murmushi ya ce "Mutum, mai zuciya cike da muradai kamar ka. Ƴan kwanakin nan ka fi mayar da hankali a kan sanin wanene ni, fiye da abun da yake damun zuciyarka. Ka bi a hankali kar garin kallon ruwa kwaɗo ya yi maka ƙafa, kar ka saki reshe ka kama ganye, ya kai wannan maciji mai hatsarin gaske" Al-amin ya numfasa ya ce "Ni ba karen farauta bane ba, da za ka din ga wasa da ni, tamkar ɗan kwiwiyon da ka raina, ka yi a hankali da ni, ƙarfe nake cikin wuta, na fi ƙarfin ɗauka da hannu" Ya sake murmusawa ya ce "Ka huta mutumina, ka samu abun da zai ɗebe maka kewa, ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, ba za su taɓa rabaka da damuwa ba, matuƙar ba ka yi abun da zuciyarka ke gaya maka ba, haryanzu ka na da sauran ƙuruciyarka, zaka iya amfanar da al'ummarka" Kafin Aminu yayi magana, mutumin ya katse wayar. "Amma Yallaɓai, kana ganin wannan abun da muke yi shi ne dai-dai? Akwai abubuwa da yawa da yakamata ace mun mayar da hankali a kai, ba bawa ɗan daba kariya ba" Ya ajiye jaridar hannunsa ya ce "Kalle ni da kyau, ba na abun da babu manufa a kansa, dan haka kawai ka saka ido" Waya ce ta fara ringing, ya ɗaga sannan ya miƙo masa. Ya karɓi wayar tare da yin sallama. "Wa'alaikum Salam, barka dai ya ƙoƙari?" "Alhamdilillah sir, an yi clearing matsalar jiya, duk da an kusa samun akasi, yaron ba ya ji ko kaɗan, idan aka cigaba da tafiya a haka, kar asirinmu ya tonu fa, dan hakan tamkar yi wa doka karan tsaye ne, mu na saɓa ƙa'idar aiki" Yayi murmushi ya ce "Kar ka damu, doka ce ta fara yi wa yaron karan tsaye, shiyasa nake amfani da dokar, wurin bi da komai" "Haka ne sir, amma fa police suna neman shi ne ruwa a jallo, mu kuma muna kare shi, muna taka doka da yawa" "ASC, ko sun kama Al'amin, ba zasu bari doka ta yi aiki a kansa yadda yakamata ba, za su bar shi da masu son zuciya ne, su yi abun da suka ga dama da shi, ba wai hukumar ce kawai take nemansa ba, akwai lauje cikin naɗi ne a neman da ake yi masa" ASC ya numfasa ya ce "Shikenan, amma laifukansa sun yi yawa, duk wani ta'addanci da za'ayi a garin nan sai ka ji yaransa ne, slide mistake za'a iya kama shi, duk da wani abun kuma idan muka bincika, sai mu tarar ba shi ɗin ba ne ba" "Haka ne, amma idan an kama shi ma, sunana na ko naka, babu wanda zai fito, haryanzu bai san ko ni waye ba, kuma ba zan bari ya sani ba, kuma yana aikata wasu laifuka ne dan ya tilasta na ƙyale shi, ko kuma na bayyana kai na a gare shi, amma ka rabu da shi, komai cikin tsari nake yin sa, ka bar police su cigaba da neman sa, hukumarka kuma ta cigaba da aikinta, kamar yadda na ce maka" Ya amsa da "Shikenan sir, am always loyal to you, na gode" "Yauwwa ASC, duk halin da ake ciki dai, ina buƙatar ka sanar da ni" "No problem, sai an jima" bayan sun yi sallama, yayi wata irin dariya, da shikaɗai ya san ma'anarta ya ce "Wannan shi ne jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya" yayi maganar yana kallon yaronsa da yake tsaye yana kallon sa. Ya ce "Lallai, amma zan so in ji wani irin shiri ne haka ka ke yi sir" "Za ka gani a aikace, kai dai ka cigaba da biyayya ga abun da duk na umarce ka, nima zan yi amfani da ƙarfin iko da kujerata, na yi abun da ya dace". "Ok sir, in sha Allah". *** Misalin ƙarfe takwas na dare, wasu daga cikin manya na ƙungiyar ƙato da gora na unguwar suka tattaru suka zauna meeting a cikin ɗan madaidaicin office ɗin su. Duba da abun da ya faru, na faɗan daba da aka yi da yaran Aminu da na Madaki a waccan unguwa, sanin ya na shigowa unguwar lokaci zuwa lokaci, sannan kuma akwai yaransa a unguwar, ya sanya su zaman yin meeting, dan ƙara ƙarfafa tsaro a cikin unguwar su, kar su gama da can su dawo nan. Suna tsaka da tattaunawar, wasu zaratan matasa suka yi sallama, suka amsa suna bin su da kallo. Suka shiga cikin office ɗin, suka kewaye su, duk suka tsaya suna kallon su. A hankali ya sauke face mask ɗin fuskarsa, a take suka shaida shi. Kafin su yi magana ya ce "Awa ɗaya rak nake buƙata, zan gama abun da ya kawo ni na fita, muddin na kuma shigowa unguwar nan, ku ka sako ni a gaba, kamar kare za ku kama ni, wallahi sai na yi muku abun da na yi wa malam lawan". Shugaban ƴan sintirin ya ce "Dan meyasa zaka din ga shigo mana unguwa? Kai da hukuma take nema ruwa a jallo, ka san kai tauraruwa mai wutsiya ne, duk in da ka je sai ka yi fitina, tun da yaranka suka yi ɓarna jiya, na san cewa nan ma zaka shigo. Duk ka lalata mana yara ka tafi ka barmu da masifa, kuma yanzu ka dawo kana cigaba da bibiyarmu" Cikin tsawa Walid ya ce "Kai, ka iya bakinka, wallahi ko na ɓare maka shi har ƙeyarka". Cikin tamkakiyar fuskarsa Viper ya ciro zungureriyar wuƙar da take ƙugunsa, ya karta ta a ƙasa tayi wata irin ƙara, sannan ya ɗora ta a gefen wuyan mutumin ya ce "Ƴaƴanku za su cigaba da yi mini biyayya, sai na mayar da unguwar nan mafi munin sansanin ta'adancci da zubar jini, komai ya faru ai ku kuka so, yanzu dan Allah kai ba ka ji kunyar faɗar abun da ka faɗa ba? Duk in da zan je zuciyata na tsakiyar unguwar nan, kuma zan cigaba da shiga da fita yadda nake so, har sai na yi maganin azababbiyar ƙishirwar da ta addabi ruhina. Duk abun da na aikata muku na ɓarna, ku kuka so, mutanen banza masu butulci, kun taki sa'a da nake dakon alƙawari mai nauyi a kaina, ban da haka tun a fitowa ta, ɗaya bayan ɗaya zan yi muku kisan gilla. Idan na sake shigowa unguwar nan, kai da wannan mutanen, ku ka yi yinƙurin yi mini wani abu, duk wanda na kama, zai zama mutum na farko da zan yi wa yankan rago!" Gaba ɗaya suka zuba masa ido, suka kasa ko motsin kirki, saboda yadda suka zagaye su da miyagun makamai. "Ku karɓe wayoyinsu, ku rufe mini su, ku saurari order da zan bayar. Duk wanda yayi muku gardama ku karya mini ƙafarsa, ko ku tsarge masa cinya". "Angama boss" Yana fita daga office ɗin, suka mayar suka rufe, suka ƙwace musu wayoyi, sannan suka tsaya a kansu da wasu irin zabga-zabgan wuƙaƙe, kamar a abba tuwa. Babu wanda ya iya wani ƙwaƙwƙwaran motsi, dan a yadda matasan suke muzurai, kuma shaye-shaye ya huda su, duk umarnin da ya ba su za su bi. Sannu a hankali yake tafiya, har ya kawo cikin layin, ya tsaya a ƙofar wani gida, ya shafe tsawon lokaci kawai ya zubawa gidan ido, yana zancen zuci, daga bisani ya ƙarasa ya ƙwanƙwasa na kusa da shi, ya ja mask ɗin sa, ya rufe fuskar shi. Yaro ne ya fito ya ce "Waye?", ya cewa yaron "Ka je ka cewa babanka an zo duba shi" Mintuna kaɗan yaron ya dawo, ya ce ya shiga. Bai yi sallama ba, haka ya kunna kai cikin gidan, har tsakiyar falon maigidan, ba tare da an yi masa iznin hakan ba. Daga maigidan har matar gidan, da ƴan matan yaran, tsuma suka hau yi, ganin wanda ya shigo har cikin gidansu. Ya zaro wuƙarsa ya ajiye a gaban malam lawan, sannan ya ɗaga wani mukulli ya ce "Na rufe gidan nan da kwaɗo ta ciki, kuma duk wanda ya yi wani ƙwaƙwƙwaran motsi, zan zaunar da shi kamar yadda na zaunar da kai" yayi maganar yana kallon malam lawan. Ya durƙusa kama ƙafar malam lawan, da aka naɗe da bandeji, ya dudduba sannan ya ce "Ɗori yayi kyau, sai dai na yi mamakin yadda aka dawo da kai gida, maimakon ka yi jinya a asibiti" ya saita tsinin wuƙarsa a cinyar malam lawan ya ce "Waye ya ɗauko ka daga asibiti?" Cikin tashin hankali matarsa ta fara kuka ta ce "Dan girman Allah Aminu kar ka yi masa wan.... "Wallahi ki ka sake magana, sai na karya ɗaya ƙafar, ka gaya mini kafin na huda cinyarka" yayi maganar cikin razananiyar muryarsa. Cikin matsanancin tashin hankali ya ce "Wallahi wasu mutane ne, ban san su ba, su ne suka sauya mini asibiti, lokaci zuwa lokaci, suke zuwa da likitansu ya duba ƙafata, kuma sun gargaɗeni a kan muddin wani ya ji kaine ka yi mini haka, sai sun kashe ni" "Waye ya kai ka asibiti ranar da abun ya faru?" Cikin kyarma da rawar murya malam lawan ya ce "Wallahi kana barin wurin, ina wannan kakarin, wani ya zo yayi mini kashedin muddin na ce kai ne zai kashe ni, ya watsa mini wani abu, ban sake sanin in da kaina yake ba, sai da safe maƙwabta suka tsince ni, na ce masu masu ƙwacen waya ne suka yi mini" Aminu ya ware masa jajayen idanunsa sosai ya ce "Idan na samu labari  akasin abun da ka gaya mini, kar ka manta take na, maciji nake mai mugun dafi, sai na maka karayar da ba zaka sake taka ƙafarka ba a doron duniya. Zan cigaba da zagayowa zan kuma cigaba da sanya maka ido. Kar ka manta ka yi mini ganganci daban-daban, na kawar da kai, na riƙe biyu a raina idan ka yi na uku kasheka zan yi har lahira". Malam lawan ya jinjina kai, yana jin yadda mararsa ta cika fam da fitsarin tsoro. Viper ya a miƙe ya juya ya bi hanyar fita. Sai da suka tabattar da tafiyarsa, sannan matar malam lawan ta ce "Na shiga uku, baban su Amir dan Allah meya aike ka sake shiga sabgar mutumin nan? Daga ƴan sandan har ƴan ƙato da goran kar wanda ya ƙara tambayarka abu a kansa ka ce ka sani, kalli bala'in da ka jefa mu a ciki?" "Ke dalla rufe mini baki, tun da yanzu na tsira da raina shikenan, ina ga sayar da gidan nan zan yi na bar unguwar, idan ba haka ba wataran kasheni zai yi " "Ai koma menene Allah ya ƙara wallahi, abun da ka yi wa bawan Allah nan ka yi butulci da yawa" "Au so ki ke na rufawa mutumin banza asiri Haule? Ni ki ke gaya wa haka?" "Oho ai gaskiya ce" haka suka cigaba da faɗa, tana mita da ɗora masa alhakin janyowa kansa ko ma menene. Aminu kuwa, ta waya ya ce wa su ɗan mama, su baro ƴan vigilante ɗin, su bi shi gida. A gidan suka tarar da shi, ya dubi Walid ya ce "Ka yawaita survey a cikin unguwar nan, mutumin nan ya tabattar mini da cewa, wanda suka canza masa asibiti, suna zuwa da likta har gida yana duba shi". "To shikenan Oga, in sha Allah za ayi yadda ka ce" "Kuma na san mutanen nan ne, da mutumin yake kirana a waya, ya zama dole na san waye, da kuma manufarsa a kaina, da yake bibiyata har haka". Walid ya ce "An gama maigida" Nabila kuwa tun da ta shiga aiki tana office ɗin ta, suna communicating da Yaya Nasir. Wayar sumayya ce ta shigo ƙaramar wayarta, dan haka ta ajiye ta hannunta ta ɗaga da sauri ta ce "Sunayya yaya ake ciki?" "Kamar dai yadda na yi tsammani" ta bata amsa. "Me ki ka yi tsammanin? Yi mini gwari-gwari" "Ba irin labarin da suke buƙata ba kenan, hakan ka iya kawo musu naƙasu ga cigaba da kuma tasirin gidan radiyon su, kuma wai ba ni da cikakkiyar shaidar abun da na faɗa" "Haba Sumayya, ni ina da shaida fa, ga kuma yaya Nasir ma, kuma ya zaki tsaya a wurin wannan shashashar matar da ba ta son cigabanki? Ki yi wa Manager magana mana direct, nima ina da lambarsa, sai na yi masa magana". Sumayya ta ce "Nabila kenan, duk kanwar ja ce, shi ne ya jaddada mini hakan da kansa". "Allah wadaran naka ya lalace, Yanzu sumayya shikenan zuba ido zamu yi? Babu wani abun yi?" Sumayya ta ce"Idan na matsa zan iya rasa aikina, abun da ya nuna mini kenan, wai ba za su iya jayayya da hukuma ba, kuma na kawar da kaina a kan abun da ba zan iya jurewa ba, da ina da wata hanyar samun kuɗin, da ajiye aikin nan zan yi Arfa" "Shikenan, zamu yi magana anjima, see you later" ta ajiye wayar ta zauna ta yi shiru. Wani irin tsaki ta ja, tana mamakin yadda galibin private organizations suke buɗe wurare, for their personal interest kawai, kodayeke na gwamnatin ma menene, duk ɗaya. Ganin ɓacin ran ba zai amfanata komai ba, tana da abubuwan da yakamata ta yi, ya sanya ta fita ta tafi office ɗin Barrister Habib. Yana ta aiki a system, ya ɗago ya amasa mata sallamarta, ya cigaba da aikinsa. "Barka da aiki barrister". "Yauwwa" ya amsa a taƙaice. "Barrister wai haryanzu fushin ka ke yi, na shiryu fa na daina duk wani abu da nake yi, sonake na zama cikakkiyar lawyer abar koyi ga wasu, kamar gwanata Barrister Naja'atu Bunkure" da ɗan sauri ya ɗago ido ya kalleta ya girgiza kai ya ce "No wonder, shiyasa ba zaki cigaba ba" "Subhanallah, meyasa?" Tayi maganar tana ware ido. Maimakon yayi magana, sai yayi mata shiru. Wani irin kallo tayi masa, a zuciyarta ta ce 'Sai fa ka yi magana barrister' A zahiri kuwa ta ce "Ni dai haka kurum nake sonta, ayyukan ta na jin ƙai suna burgeni, ina son zama kamar ita. Amma tun da haka ne ma, na canza kamar kai nake son zama, daga yau kai ne mudubina" tayi maganar tana murmushi. "Ke da ba zaki iya zalunci ba, mu ne azzalumai ai" Nabila ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, waye ya faɗi haka? Wallahi ba haka bane ba, ni ban ce ba" "Idan har kina son zama shahararriya, dole ki yi iya yinki, a kan duk abun da ya zo hannunki, ko da kuwa babu tabbacin zaki yi nasara, idan ba zaki iya ba kuma, you can leave" "No, zan iya, ai na shiryu yanzu" Ya buɗe drower gabansa, ya ɗaukko wani file ya ajiye mata sannan ya ce "Wannan client ɗi na ce, a nan ƙofar na'isa gidanta yake, zan turo miki cikakken adress ɗin ta, ki je ku yi magana, sannan ki yi tunani a kan case ɗin nata" Cikin girmamawa ta ce "Na gode sosai, zan yi in sha Allah " Tana fita daga office ɗin nasa, ta gyatsine baki, ta ce "Kamar ni za a aika, gidan wata ƙatuwa, ba ma ta zo office ta same mu ba, hamshaƙiya saboda ga ƴar Nabila ƴar wahala. Amma bakomai da na zama abun da nake so, na fi ƙarfin kowane irin wulaƙanci" ta koma nata ofishin tana cigaba da ƙunƙuni. Da ta koma gida ma, ba ta bi ta kan aiken da barrister yayi mata ba, ta kwanta ta sha baccinta, bayan ta tashi ta shirya ta yi wanka, ta tafi gidansu sumayya. Sun jima suna tattaunawa da sumayya, a kan harkar aiki, har sumayya ta din ga ja mata kunne, a kan kasadar da take yi, tare da nuna mata illar hakan a matsayin ta na ƴa mace, ta kunnen hagu maganganun sumayya suka din ga shiga kunnenta suna fita, dan ba ta ji sun shigeta ba. Ta bawa Sumayya labarin aiken da barrister Habib ya yi mata. Sumayya ta ce "Kuma zaki ɗin?" "To ya zan yi?" Sumayya ta yi dariya ta ce "Ai na zata taurin kan yana nan?" Nabila ta yi murmushi ta ce "Na ajiye taurin kai, zan kama aikina yadda yakamata, ai sai burina ya cika sai na binciko wacece Bunkure kuma in sha Allah, sai sunana ya shafe nata a tarihin duniyar ma'abota shari'a". "Allah wadaran naka ya lalace, Nabila, wai ke wani irin taurin kai ne da ke ne? Ke abu ba ya wucewa a wurinki ne? Ki bar ta kawai, idan Allah ya so, tana raye zata ga nasarar da zaki yi a rayuwa" "Ina kwance nasarar za ta zo ta same ni kenan? Ke ƙyaleni, ina ga sai Allah ya kaimu friday da yamma, zan je waccan unguwar gidan matar, na ga bai turo mini contact ɗin matar ba tukuna, zaki rakani?" Sumayya ta ce "A'a gaskiya, wannan unguwar, ana ta fama, kamar ba kya jin radiyo, yadda suke fama da faɗace-faɗacen daba. Ki gayawa barrister ya ce  kawai matar ta je office ɗin ku, ko kuma ki bari komai ya lafa, dan kullum cikin faɗan daba suke" Nabila ta ce "So ki ke in kasa samun information ɗin da nake so daga bakinsa kenan? Ai lallaɓa shi zan tayi, sai na san wacece matar nan. Kodayake ma na saka Yaya Nasir ya rakani" sai kuma ta yi shiru, ta sake maimaita zancen Sumayya a zuciyarta. *Wannan unguwar ana ta fama da faɗan daba* Ta sake kallon sumayya ta ce "A unguwar ne aka ce yaran Aminu Viper sun yi sare-sare?" Sumayya ta yi shiru tana kallon idon Nabila. Nabila ta yi murmushi ta ce "Kar fa ki kawo komai a ranki, ba wani abun zan aikata ba, bari na tafi kan Abba ya dawo ya nemi ina nake" ta ɗau jakarta ta fita, tana jin kamar matsalarta ta zo ƙarshe. *Masu nema daga farko, ku yi joining link channel ɗina na saman page, idan kun shiga zaku samu daga farko* Arewabooks ayshercool7724 Watpad ayshercool7724 Ayshercool 08081012143 [7/21, 2:16 PM] null: *ƘARFE A WUTA* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION BRIGHT PENS SECOND BATCH https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g 7 Katafaren falo ne, wanda girmansa ya ishi wani talakan gina gidan da zai rayu a ciki, talabijin ɗin da ke falon kawai ta fi rabon bango. Kujera set biyu ce a falon, kuma tsakanin kowane set da wani akwai tazara. Tinkis-tinkis haka ya fito cikin wata irin dakakkiyar shadda maroon, sai ƙyalli take yi, ba sai an faɗa ba ka san akwai tazara mai nisan gaske tsakanin sa da talauci. Ba wata ƙiba ce da shi ba, amma cikinsa yayi kurtsitsi a riga, har wani nishi yake yi. Ya nemi wuri ya zauna a ɗaya daga kujerun falon, ya kalli matasan da suke zaune a ƙasa a kan carfet. Dukkansu babu mai suturar kirki a cikinsu, kansu duk askin banza, yanayin shigarsu da fuskarsu kawai za ta tabattar riƙaƙƙun masu laifi ne. "Allah ya taimaki maigida" cewar ɗaya daga cikin su. "Ya aka yi madaki?" "Akwai ƙura ne, ƙurar kuma na neman zama gagarumar guguwa" "Ina jin ka" "Aminu Viper, haryanzu jami'an tsaro ba su kama shi ba, ya sa an kaiwa yarana mummunan hari, an yi musu miyagun raunuka, jami'an tsaro sun kama yarana sun saki nasa, wanda aka kai asibiti ma, an kwashe su daga asibiti babu wanda ya san in da aka kai su" Mutumin yayi tsaki ya ce "Ina mamakin yadda mutum ɗaya ya gagari kamun hukuma, ni anya ba raina mini hankali ma suke yi ba a kansa? Yanzu menene abun yi?" "Ka saka a sakar mini yarana, dan sai da su ayyukanka suke yiwuwa, kuma dole mu yi shiri sosai, idan da hali mu mu nemi in da yake mu kashe shi kowa ya huta" Mutumin yayi shiru yana kallonsa sannan ya ce "Aikuwa da na yi maka tukucin da baka taɓa tunani ba, zan saka a saki yaran nan anjima kaɗan, sai dai duk yadda zaka yi ka yi, a samo yaron nan, dama mugu shi ya san makwantar mugu ai" Madaki ya sauke numfashi ya ce "Zan shirya gagarumar ɗaukar fansa kan mai uwa da wabi a unguwar su, jinin yarana da suka zubar ba zai tafi a banza ba, dan shammatar su ka yi, suka mamaye su ba na nan" "Wannan ku ta shafa, ni babban burina shi ne Aminu, muddin yaron nan yana numfashi, kamar sarƙa ce a wuyana, dole a kawar da shi". Madaki ya ce "Ba kai kaɗai ba, ko kuma in ce da ni da kai kusan abu ɗaya ne a wurinsa, nima ka san akwai tawa ni da shi, tsohuwar gaba ce ta tsawon shekaru, wanda a kanta unguwanninmu suka kasa zaman lafiya har yau, ga kuma wannan al'amari da ya faru. Muddin ban kashe Aminu ba, ni zai kasheni" Ya jinjina kai ya ce "Ai Viper na fuskanci ƙarfe ne a wuta, ya fi ƙarfin ɗauka da hannu, sai dai da ɗan uwansa ƙarfe, kai kaɗai zaka iya maganinsa" "Ka bani lokaci kawai, zan kuma ƙoƙartawa, matsalar ko yaransa ba kowa ne ya san in da yake ba, amma na san dole Walid ya san in da yake, amma shi ma Walid ba lafiya ba ne taɓa shi, ka dai bani lokaci" "Babu isasshen lokaci, ka yi huɓɓasa kawai" Madaki ya jinjina kai. Mutumin ya ɗebo kuɗi ya bashi, ya sallame su, suka juya suka fita da shi da yaransa. Nasir ne tsaye a office ɗin sa, ya kalli matashin da yake zaune, da aƙalla zai yi sa'ansa ya ce "Mu'azzam lamarin ƙasarmu sai Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ka san da ƙyar na gano station ɗin da yaran nan suke, ba ma ta yankin da abun ya faru ba ce?" Mu'azzam ya yi murmushi ya ce "Haka ka ce mini" "Gaba ɗaya yaran under age ne, kuma duk cikinsu babu yaran Aminu, dan tuni an sake su, sai wani wai madaki, na ce dai a ajiye mini su, da yiwuwar mu kama madakin, zai iya sanin in da Aminun yake,tun da abokin faɗansa ne, amma da na yi magana da DPO ɗin division ɗin yankin, ya ce shi ma madakin ba ya kamuwa, kuma ya addabi yankin yana da yara sosai da sosai. Abun takaicin ma ba unguwar su ɗaya da Aminun ba, amma suke cigaba da tayarwa da mutane tarzoma" Mu'azzam ya ce "Harkar nan tamu sai fa Innalillahi wa Innalillahi raji'un, muna tufka manyanmu na warwarewa" Nasir ya ce "Bari kawai, zan yi iya ƙoƙarin da zan yi, ni zan kama Madakin, Arfa har asibitin da aka kai waɗanda aka yi wa rauni ta je, muka yi waya kafin na je wai an kwashe su, an bar asibitin da su, na fara zargin anya ba jami'an mu ne aka samu bara gurbin da suke mara masa baya ba" Mu'azzam ya ce "Ba abun mamaki bane ba, amma meya kawo Arfa cikin wannan lamari, ta bar aikin lawyern ne?" Yayi murmushi ya ce "Rigima mana, yarinyar nan ta zarce tunaninka, ba ta wasa da duk abun da ya shafe ni ko cigaba na" "Hmm Nasir kenan, wai yaushe zaka gayyacemu sabgar nan ne? Shekarun ka fa suna ja" Nasir ya rausayar da kai ya ce "Mama ce ta hana, ta nuna ba ta so, ban taɓa gaya mata ba, saboda tun kafin na furta maman ta gargaɗe ni a kan haka, kuma haryanzu ni ban ji ina son kowace yarinya ba, ita ɗin dai nake so. Ban san adadin samarinta da na kora ba saboda kishi. Yadda take son abun da nake so da son cigabana, na san da zan furta ina sonta, ba zata ƙi ba, amma na rasa yadda zan yi da mama". "A'a Nasir, dan Allah kar ka zalunci yarinya, haka zaku zauna shekaru na tafiya, kai baka aureta ba, kuma ba ka bari wani ya aura ba? Wannan ai mugunta ce, ka yi magana da Abba mana". Nasir ya girgiza kai ya ce "Manta kawai, abun ya wuce yadda ka ke tunani". *** Arfa na kitchen tana taya baba magajiya aiki, suna hira tana tambayar baba magajiya kwatancen cikin unguwar ƙofar na'isa, dan zuwa aiken barrister Habib, dan ita ba zuwa ta taɓa yi ba. Baba magajiya na girki, ita kuma tana wanke-wanke a sink. Siyama da take ƴa ta uku ga mama ce ta shigo kitchen ɗin, ta jefawa Nabila kwanukan hannunta maimakon ta ajiye. Nabila ta yi shiru, ta cigaba aikinta suna hira, duk da abun ya ɓata mata rai. Amfani ta kuma yi da kofi, ta wurgowa Nabila cikin sink, cikin zafin nama da masifa, Nabila ta ɗauki kofin ta jefa mata a fuska ta ce "Ai ba baiwar ubanki ba ce ni, da zaki din ga jifana da kwanuka" "Nabila ni ki ka daka?" "An dake ki ɗin?" Baba magajiya ce ke ƙoƙarin basu haƙuri, amma siyama ta shaƙe Nabila, Nabila ta rarumo wani kwano ta buga mata, dambe ya kacame. Baba uwani ta yi ƙoƙarin raba su, amma abu ya gagara. Ta fito falo da gudu, tana neman taimako. Dambe tun daga kitchen har falo, duk abun da Nabila ta rarumo sai ta kwaɗa mata, kamar wasu kuraye. "Mahaukaciyar ina ce ke? Ke kullum haka zaki ƙare ki zagi wannan ki ci mutuncin ƴaƴan gida kina ƴar karere" Cikin baƙin ciki Nabila take kallon mama, tana iya ƙoƙarinta wurin danne abubuwan da mama take yi mata, duk faɗanta da tashin hankalin ita da yaran gidan suke yi, amma sai mama ta shiga ta zaƙe ta shigarwa yaranta. Anty ta ce "gaskiya maman Sauda wannan ba girmanki bane ba, maimakon ki yi musu nasiha, sai ki din ga aibata Arfa, ai ba a haka" Siyama ta din ga zagin Nabila, zagi na cin mutunci, tsawar da Abba ya yi musu ne, ya sanya duk suka ɗago cikin tsuma. Ya nuna nabila ya ce "Arfa, ban isa na saka doka ki bi ba ko? Siyama ba gaba take da ke ba? Nake jiyo muryarki tun daga waje kina zaginta?" Arfa ta buɗe baki zata yi magana, amma ya daka mata tsawa ya ce ta yi masa shiru. Siyama kuma ta fashe da kuka tana gaya masa har dukanta arfa tayi. Aikuwa ta in da ya shiga ba ta nan yake fita ba, ya hana kowa magana ya yi wa arfa kaca-kaca saboda sanin ba ta ji, ga rashin haƙuri da taurin kai. Da sauri ta tafi ɗakinsu tana wani irin kuka, ta je ta faɗa kan gadonta, jikinta har rawa yake yi saboda baƙin ciki takaici ta din ga kuka. Cikin kuka ta ce "Ya Allah ka bani miji kowane iri ne, in dai zai zama alkhairi a gare ni, na tafi na bar gidan nan, na gaji Allah ka amsa mini dan girmanka, kowane iri ne zan iya zama da shi". Can falo kuma, jikin Abba ne yayi sanyi, ganin arfa na kuka ya san akwai wani abu a ƙasa, dan idan tayi laifi, wataran ko kasheta zai yi ba zata yi kuka ba, duk da tana da saurin kukan. Ya kalli Anty ya ce "Zainab je ki duba yarinyar nan, kar ciwonta ya tashi" Anty ta jinjina kai, ta bi bayan arfa. Mama kuwa a sashinta take yi wa Siyama mitar meyasa ba ta yi wa Nabila dukan da za ta kasa tashi ba. "Mama kin san yarinyar nan har aljanu take yi, haka kurum su tashi ni ta kashe ni, komai ta rarumo buga mini take yi, ba ki ji kafaɗuna ba" Mama ta yi ƙwafa ta ce "Na rasa yadda zan yi maganin yarinyar nan, wallahi bana sonta ba na ƙaunarta, gaba ɗaya ba kwa gaban mahaifinku sai ita, in sha Allah sai ta zame masa masifar da ba zai iya shawo kanta ba, sai ta kwaso abun kunyar da za ta kunya ta shi a idon duniya". Nabila kuwa ƙin saurar anty ta yi, ta sha uban kuka, Anty ta sanarwa Major kukan da take yi, ya basar kamar bai damu ba, amma ƙasan zuciyarsa sam babu daɗi. Tsakar dare suke waya da sumayya, take gaya mata abun da ya faru. Sumayya ta ce "Arfa, ke rashin haƙuri ne yake janyo miki wasu abubuwan, da kin yi haƙuri ba ki tanka mata ba, dama neman magana ta zo yi". "Sumayya kin san ba zan iya ba, ni ina wulaƙanta mutane ne?" Sumayya ta ce "A'a idan na ce kina da wulaƙanci Nabila na yi miki sharri, sai dai masifa da rashin haƙuri, ga jarababben taurin kai ba a gaya miki ki ji ko kaɗan" Nabila ta ce "Sai dai ayi haƙuri da ni a yadda nake, ni ba zan yadda da wulaƙanci ba" "Aikuwa zaki yi ta shan wahala dan ubanki" Nabila ba ta damu da zagin da sumayya ta yi mata ba, domin idan da sabo ta saba, dan wasu lokutan sumayya playing role take yi kamar na uwa a rayuwarta, ta kan ji maganarta idan ta ga dama. "Sumayya dan Allah ki yi mini addu'a, Allah ya bani miji kowane iri ne, in dai zai zame mini alkhairi a shekarar nan na bar gidan nan na huta" Sumayya ta ce "Ba ki da hankali, kowane iri fa ki ka ce" "Eh, wallahi idan ba haka ba, zan gudu na bar garin nan, na bar musu gidan, sumayya baki san me suke yi mini ba na gaji" ta ƙarasa maganar cikin shagwaɓa tana kuka. Sumayya ta san komai, dan haka cikin rarrashi, ta kwantar da murya, ta din ga yi wa Nabila nasiha, da rarrashin ta, har ta sassauta kukan da take yi. Da haka suka yi sallama, ta kwanta bacci. Sai dai ta kasa baccin, saboda yadda zuciyarta take zafi, ta rasa me ta tsarewa maman su Sauda a rayuwa, da ita da yaranta suka tsaneta haka, Nasir ne kawai suke ɗasawa da shi, da ƙyar bacci ya kwashe ta. Da safe ta shirya cikin wata abaya baƙa, tayi kyau ko karyawa ba ta tsaya yi ba, ta fito falo fuskarta babu walwala. Kallo ɗaya zaka yi mata, ka san ba ta samu isasshen bacci ba. Da kamar ta yi fuska tayi tafiyarta, amma ta haura benan Abba ta je ta gaishe shi, sai dai fuskarta babu annuri, babu raha da ta saba yi idan ta je gaishe shi. Ya ƙura mata ido ya ce "Kin karya kuwa?" Ta ce "Idan na tsaya karyawa zan makara, zan karya a wurin aiki" "Dan zaki makara sai ki fita ba ki karya ba, yaushe ki ka fara tsoron makara? Menene ma ya hana ki tashi da wuri?" Tayi shiru tana wasa da yatsun hannunta, idonta yana cika da hawaye. Ya saka hannu a aljihunsa, ya ciro kuɗi masu yawa, ya miƙa mata ya ce "Ga wannan na san wata yayi nisa, babu lallai ki na da kuɗi a hannunki, ki sai wani abun idan kin je ki karya, saura ki sai abun da zai ɓata miki ciki, ko ya cutar da lafiyar ki" Kamar ta ce ya bar su, amma ta saka hannu biyu ta karɓa, ta ce ta gode, yanayin yadda take tafiya kawai, zai tabattar mata da tana cikin damuwa ko rashin lafiya. Gaba ɗaya jikin Abba ya yi sanyi, a tsakiyar zuciyarsa yake jin zafi, idan ya ga Nabila a cikin damuwa, shiyasa wasu lokutan baya iya jure yi mata hukunci yake kawar da kai a kanta. Duk iya ƙoƙarin da Nasir yake yi, a kan yaƙi da harkar daba, abu ya ci tura, dan yaran da aka kama ya koma ya tarar da wai an yi umarni daga sama a sake su, abun ya ɓata masa rai sosai da sosai. ***** A farfajiyar wata bishiya suke zazzaune, suna ta shaye-shayen kayan maye, duk sun cika wurin da ƙaurin hayaƙi. Madaki ya karta wuƙa a ƙasa, ya kalli tarin matasan da sun fi ashirin a gabansa ya ce "Babu rangwame ko sassauci, babu mace babu namiji, ko babba yaro ko tsoho, duk wanda aka samu idan aka shiga operation ɗin nan a farmasa, ayi ɓarna ayi ta'adi a ɗauki fansar abun da Aminu yayi mana, jini ya din ga gudana ko ta ina, duk shagon wanda aka samu a fasa ku kwashi ganima, na yarje muku. Haka zalika duk wanda ya gano in da Viper yake, muddin ya kawo mini shi, a mace ko a raye, akwai tukuici mai tsoka" Suka fara shewa cike da maye, ɗaya daga cikin su ya ce "Aminu fa ƙarfe ne a wuta, duk wannan shewar kama shi ba abu ne mai sauƙi ba, da mai sauƙi ne na san da ka riga mu kama shi" Madaki ya ce "Rufe mini baki, ko na yi gunduwa-gunduwa da namanka, dole ne a kama shi, kai gobe duk wanda aka gani daga tsallaken unguwar su, ya shigo unguwar nan ma a sara mini shi kawai, a ɗauki fansa mafi muni na abun da ya yi mana, zan ga da ni da shi, waye zai sarara waye gaba da wani" Cikin haɗa baki suka dinga faɗin "An gama oga, gobe akwai ƙaramin yaƙi" misalin ƙarfe sha ɗaya da rabi na safe, a sannu take tafiya a cikin unguwar, tana duba kwatancen da barrister Habib ya tura mata. Kasa ganewa tayi, ta tsaya a wurin wani mai kanti, ta sayi ruwa ta sha, kuma tambaye shi. Tana tsaye tana duba wayarta a cikin shagon provision ɗin, wani matashi ya shigo, suka gaisa da mai kantin ya ce "Bani ƙulli biyu da ruwa uku" Mai kantin ya ce "Amma ka san ina binka sauran kuɗi ko?" "Zan biyaka, wannan yawa ne, ka bani na ware mana, caji zan yi kaina gaba ɗaya babu network,aljihuna kuma yayi gobara" "Ba zan bayar ba" mai shagon yayi maganar yana miƙawa Nabila ruwan roba. Nabila ta din ga satar kallon matashin, yadda bakinsa ya karkace saboda shaye-shaye take kallo, laɓɓansa duk sun zazzago. Tayi gyaran murya ta ce "Ɗan uwa ka bashi mana, tun da ya haɗaka da Allah, in sha Allah zai kawo maka, tun da ya yi alƙawari" "Rabu da shi, ba ya biyan bashi" Nabila ta yi murmushi ta ce "Nawa ne kuɗin nasa?" Mai kantin ya ce "Dubu biyu nake bin sa" Ta yi murmushi, tare da ciro kuɗi a jakarta ta ce "Dubu biyu ai babu yawa, Ga dubu uku, na biya masa kuɗin da ka ke bin sa, ka bashi wani bashin, ni kuma ka ɗauki kuɗin sayayyata" Matashin ya kalleta ya ce "Sai kin yi babbar yaya, Allah ya ƙara arziki" Ta amsa da "Amin ɗan uwa na gode sosai". Wani abu ta ga an bashi a nannaɗe a leda, da ruwa ya sake yi mata godiya, ya fice. Yana fita ta ce "Malam dan Allah menene wannan ya saya?" Mutumin yayi murmushi ya ce "Ƙanwata wiwi ce" waro ido ta yi ta ce "Wiwi kuma, ka ke sayarwa? Amma na ga kai kamar ba ka sha ko?" "Ki yi ƙasa da muryarki mana, ya zamu yi sana'a ce, ni ba abun da nake sha. ga canjinki" Cikin mamaki ta ce "Meyasa ka ke sayar da abun da ba ka sha?" "Kar ki tsananta bincike malama" yayi maganar yana haɗe rai. Ta jinjina kai ta ce "To Allah ya taimaka" Fitowa ta yi daga shagon, ta hangi matashin yayi nisa, ta rufa masa baya ta bishi da sauri. "Bawan Allah ɗan tsaya dan Allah" ta ƙarasa tana haki. Ya tsaya yana kallonta ya ce "Ya dai?" "Abu zan tambaye ka, amma kafin nan ka san abun da ka saya ɗin nan, yana da illa ga lafiyarka?" Tsayawa yayi yana kallon ta, tayi saurin cewa "Dan Allah taimako nake nema, wani gida nake nema, amma na kasa gane layin, ko zaka taimaka mini?" "Ina ne?" Ta gaya masa ya ce "Na san gidan, amma ba hanyar ki ka biyo ba nan" "Dan Allah kwatanta mini" "Mu je na kai ki bakin layin" Ta ce "Yauwa ɗan uwa, dan Allah mu yi wata magana mana, ka san wani mutum Aminu Viper?" Wani irin burki ya ci yana kallonta. "Yi haƙuri idan na ɓata maka rai, ɗan uwana ne shi, tun da Allah ya sa ya bar gidan yari, bamu sake ganinsa ba, kuma na ji an ce yaransa sun tayar da tarzoma a unguwar nan a satin nan, dan har asibitin da aka kai waɗanda aka yi wa rauni na je, na zaci zan ganshi, amma ban tarar da shi ba" Ya ware mata jajayen idanunsa ya ce "Ki ka ce ɗan uwanki ne?" Cikin ƙarfin hali ta ce "Eh, ina da alaƙa da shi" Ya ce "Na san shi, na kuma san in da yake" Da sauri ta ce "Dan Allah ka taimaka mini a ina zan ganshi?" Ya ƙare mata kallo ya ce, idan kin tashi, ki tambayi ina ne layin iraƙi a unguwar nan, idan ki ka je akwai wata babbar bishiya zaki ga wasu a zazzaune a wurin, ki tambaye su, za su nuna miki shi. Cikin tsananin farin ciki, ta din ga yi masa addu'a. Amma fa sai dai ta kasa tantance irin kallon da yake yi mata, hakan bai dame ta ba. Har ƙofar gidan matar ya rakata, ta kuma yi masa godiya, ta ciro kuɗi ta bashi, sannan ta shiga gidan matar. Matar ta karɓi Nabila hannu bibbiyu, bayan da Nabilan ta yi mata bayanin barrister Habib ne ya turo ta. Ta bawa Nabila duk wani information da take buƙata, tana gama abun da take yi ta tashi ta ce tafiya za ta yi. Babu yadda matar ba ta yi da ita ba, a kan ta zauna ta ci abinci ta yi salla, amma taƙi, ta tashi ta tafi. Babu tunanin komai, tana fita, ta tambayi wasu yara, ina ne layin iraƙi?. Duk sai da suka kalleta, ganin tana mace tana tambayar wannan layin da ƴan daba suka mayar mallakinsu, abunka da yara, babu tunanin komai suka sakata a hanya, ta yi musu godiya ta nufi kwatancen. Tana ta addu'a Allah ya sanya ta dace, duk tana da burin cikar nata muardin, amma za ta yi farinciki sosai idan aka ce Nasir ne yayi nasarar kama Aminu, koba komai likkafarsa za ta sake ɗagawa, ta nufi layin ba tare da ta san idan ta ganshin me za ta ce masa ba. Layin shiru babu kowa, babu gina-ginan kirki, sai kangwaye, sai da ta je tsakiyar layin, ta hango wata ƙatuwar bishiya, da mutane. Kamar ba mace ba, babu razani ko fargaba ta tunkari bishiyar. Gaba ɗaya suka zuba mata ido, har ta ƙaraso. Wiwi kawai suke busawa, ta ɗan tsaya nesa kaɗan da su, saboda hayaƙi. "Ina wuninku" Suka amsa mata da lafiya ƙalau, suna mamakin ganin mace a wannan chamber. "Dan Allah tambaya nake yi, wani nake nema, aka yi mini kwatancen nan aka ce zan sameshi". Ɗaya daga cikin su ya ce "Waye shi?" Ta ce "Amm, sunansa Al'amin, amma ana ce masa Aminu Viper, tun da ya fito daga prison ba mu sake ganinsa ba" Ɗaya ne ya miƙe tsaye ya ce "Ke, ba ki da hankali, a dabar madaki ki ke naman wannan ɗan iskan? Kai kan taba, sako su mass su rakata, tun kan oga ya zo ya saka ayi gunduwa-gunduwa da namanta" Sai yanzu ta fuskanci shigo-shigo babu zurfi wanda ya yi mata kwatancen ya yi mata. Cikin sauri ɗaya ya ce "Meyasa za'a bari ta tafi? Bayan ka san yau zamu fasa ɗaukar fansa, ta kanta ya kamata mu fara" yayi maganar yana ƙoƙarin zare makami. Sai dai tuni suka sako wa Nabila wasu irin murguza-murguzan karnuka, masu kama da zakuna. Cikin ihu ta kwasa da gudun tsiya, tana kururwar neman agaji, saboda yadda take ganin kamar karnukan za su cinyeta ɗanya, sai dai gudun da suke yi ya wuce hankali, ga takalminta mai tsini ne sosai, dan haka suka kusa cimma ta. Babu tsammani ta faɗi, saboda yadda numfashinta ya fara sama-sama. Ayshercool. 08081012143 [7/22, 1:49 PM] null:               *ƘARFE A WUTA* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g P8 Ta saka hannu, ta kare kanta, tana jiran su hauta da cizo. Wani irin fito ya yi wa karnukan, suka juya suka koma da gudu in da yake. Matashin nan ne na ɗazu, da ta biyawa bashi, ya kalleta ya ce "Kin san meyasa na taimake ki?" Bai jira amsar da za ta bashi ba ya ce "Ba na tunanin Aminu yana da wata ƴar uwa mace, dan haka ƙarya ki ke yi, akwai wata manufa a ranki da yasa ki ke nemansa. Sannan ya taɓa yi mini alfarma a lokacin da ya samu damar da zai kashe ni, kuma kin kyautata mini, alhalin baki sanni ba. Ɗan daba ba mahaukaci bane ba, shaye-shaye ne yake ruɗa mana tunani. Wannan shi ne kaɗan daga abun da ka iya samunki, idan ki ka cigaba da neman sa, ko bibiyarsa, wannan dabar babu abun da suke buri da fata, sama da su riga ƴan sanda kama aminu, mace ce ke ki kiyaye kanki, tashi maza ki tafi gasu can tahowa, idan suka cimmiki babu lallai na iya hana su illata ki" Da ƙyar ta tashi, ta yi gaba da sauri, tana cigaba da haki, adaidaita sahu ta hau, ta yi masa kwatancen in da zai kai ta. Kasancewar mai rabon shan duka, baya jin bari, suna tafe tana sauke numfashi, tana tunanin son sanin su kuma waɗan nan me yayi musu suke son su riga ƴan sanda kama shi, suna ƴan uwansa ƴan daba. "Ko wani ya kashe musu?" Ta tambayi kanta. "Yayi kisan kai, kuma a sake shi? Aikuwa sai na ga ƙwal uwar daka" ta furta a hankali. Ta so ta gaya wa Nasir, abun da ya faru yau, amma ta san tsaf zai ce zai zaneta, saboda kasadar da ta yi, dan haka ta bar wa ranta cewa sai ta samu wata gagarumar nasara, sannan za ta sanar da shi. Ko sumayya ma ba ta gaya wa ba, tayi shiru da bakinta, sai dai faɗuwar da tayi, duk ta goge gwiwa. Haka kurum tausayi, da tunanin makomar rayuwar matasan da ta gani, a harkar daba da shaye-shayen nan, ya dami zuciyarta ta rasa abun da yake yi mata daɗi, tana matuƙar son sanin me suke ji a cikin kayan shaye-shaye? Tabbas da ita wata ce, sai ta taimakawa rayuwar su, ko a mutum goma, idan biyu suka shiryu ai an rage. Kamar wadda ta sha kayan maye, haka yau tayi bacci da wuri, gudun da tayi jikinta duk ciwo yake yi mata, ga numfashi sai wahala yake ba ta. A wani ɗaki ta ganta, mai duhu sai haske kaɗan a ciki, ga karnuka duk a cikin ɗakin, sai haushi suke yi mata, an ɗaure su da sarƙa. Ihu take yi tana neman agaji, amma babu wanda ya san tana yi. Can sai ga wani mutum ya shigo, dogo sosai, mai cikar halitta, ba ta ganin fuskarsa saboda duhu, ya shigo ɗakin bai ce mata uffan ba, ya danƙo hannunta ya biyo tsakanin karnukan ya fito da ita daga ɗakin, ya ciro wuƙa zai caka mata a ciki. Wani uban ihu ta saki, tana kiran sunan Allah, da na Abba da Nasir. Tana buɗe ido, ta ga Abba a kanta, da Nasir, da su walida har da Anty da baba magajiya, ana ta tofa mata addu'a. Kallonsu take yi ɗaya bayan ɗaya, ta ce "Abba ya na ganku a nan? Meyafaru?" Nasir ya ce "Sannu" Abba ya ce "Arfa ba kya addu'a ko?" Ta girgiza kai ta ce "Ina yi Abba" "A'a ba kya yi, da kina addu'a babu yadda za ayi, ki kwanta kina yi mana ihu da safiyar nan, shiyasa nake hanaki wannan shegen fentin da bulbula turare a jikinki, dole sheɗanu su yi ayari, su yi ta binki" Nasir ya ce "Dan Abba ka yi haƙuri, haryanzu a tsorace take ma, a bari ta dawo hayyacinta gaba ɗaya, sannu Arfat, ki ɗauro alwala ki zo ki ɗauki Alqur'ani ki karanta". Abba ya miƙe ya ce "Aishikenan, zan yi waya da Barrister, su baki day off, ki samu ki huta" Nabila ta yi shiru tana rarraba ido, ta san lafiyarta ƙalau, tsabar tsorata ne da tayi. Tayi shiru ba ta faɗi abun da ya faru ba, suka din ga yi mata sannu. *** YALOKO ƘARAMAR HUKUMAR UNGOGGO Matashiyar yarinya ce, wadda dudu shekarunta ba su fi goma sha huɗu ba, take ta iza wuta a cikin murhu, gefe ga garin tuwo a cikin ƙwarya. Yaro ne ya yi sallama, ta ɗaga kai ta amsa masa. Ya kalleta ya ce "Ramma ki zo ana sallama" Ta ɗan waro manyan idanunta ta ce "In ji wa? Ko Habu ne?" "A'a, wani ne da mota" Ta miƙe tsaye ta ce "To mota kuma, ina zuwa?" Daga tsakar gidan ta ɗan ɗaga murya ta ce "Mama, wai ana nemana a waje, bari na duba waye, ruwan ya kusa tafasa" Daga cikin ɗaki matar ta amsa mata da "To ramma, hanzarta ki dawo, ina son zan fita ne" Ramma ta amsa da "to" ta ɗauki hijjabinta ta saka ta fice waje. Mintuna goma sha biyu ta dawo, jiki a sanyaye. Mamanta ta kalleta ta ce "Menene?" "Mama daga Kano ne, wai Anty mai jidda ce gidan da nake aiki, ta yi waya wai azo a ɗauke ni a mayar da ni, a satin nan za su dawo" Matar tayi sak ta ce "Da wuri haka, ba cewa aka yi sai bayan wata guda zaki koma ba?" Ramma ta ja ta tsaya ta ce "Jikina duk yayi sanyi, wai yanzu-yanzu zamu tafi" "To shikenan ai babu wani abu, ki yi haƙuri kin ji ramma, ni kaina ba a son raina ki ke barin gabana ba, da Allah ya sa mun tara kuɗin kayan gado, shikenan sai ki dawo ki yi auren ki. Maza mu je na tayaki haɗa kayan" Cikin abun da bai fi mintuna arba'in ba, suka haɗa kayan, suka yi sallama ramma ta bi direba zuwa gidan aikinta da yake Kano. Yana zaune ya zuba musu ido, suna haɗa masa tea, Walid ya zuba ƙwayoyi a cikin kofin, sannan ya zuba shayin. "Ƙara wannan ba zasu ɗauke ni ba" Walid ya ce "Amma boss, kai fa ka ke hanamu sha a baya, tayi yawa wallahi". "Ka ƙara mini na ce" yayi maganar a hasale. Ya ƙara masa ƙwayoyin yana kallonsa, saboda ƙwayar da suke yi wa laƙabi da raina kama, a baya sam baya shan irinta, saboda yadda take bugarwa, wasu lokutan rabi suke ɓallawa su sha, amma ya ce a saka masa kusan biyar yanzu. Ya ɗauki kofin ya kai bakinsa zai fara sha, Walid ya ce "Yau fa madaki za su je ɗaukar fansa cikin unguwa, daga majiya mai ƙarfi na ji zancen, daga jiya zuwa yau ya ce idan ɗan arearmu ya shiga ta su, a aika shi kawai" Ya cigaba da girgiza kofin ba tare da ya yi magana ba, ya sake yinƙunrin kai kofin bakinsa, walid ya sake cewa "Wata ta je nemanka a arear, aka kaita dabar madaki, Allah ne ya yi da kwananta a gaba, da kasheta za su yi" Duk da cikinsa yayi wata ƙara, jin an ce mace ta na nemansa. Wace mai tsautsayin ce wannan? Me take nema a wurina?, amma ya maze ya ɗago jajayen idanunsa ya kalli walid ya ce "Ni kuma?" Walid ya ce "Ba zan yi maka ƙarya ba, da gaske nake" Wani dogon tsaki ya ja, ya dungurar da kofin shayin, ya tashi ya ce "Ku ɗebo yaran nan na cikin unguwa, da na can wajen gari, ku sake dira a dabar madaki, ina son ɓarnar da za ku yi ta fi waccan, kar ku basu damar cutar da kowa. Ko kun gaya wa jami'an tsaro ƙudurinsu, babu abun da za su yi musu, ku far musu kawai, ka shirya komai, a bawa yaran na shan sigari" bai jira amsar walid ba ya fice. Walid ya yi ajiyar zuciya, ɗan mama ya kalle shi ya ce "Da gaske ka ke wata ta je nemansa, ko kuma ka faɗa ne, dan ka hana shi shan ƙwayar nan?" Walid ya ce "Duka, kai da ya sha abun nan, zai iya mutuwa fa" Ɗan mama ya ce "Ai rigimar da yake yi kwanan nan, ta ƙara yawa, sai an ƙara saka masa ido sosai, kashe kansa yake son yi wallahi, wasu lokutan bana son muke watsewa  mu bar shi shikaɗai a gidan nan". Walid ya girgiza kai ya ce "Ba zai kashe kansa ba". "Ya aka yi ka san hakan?" "Yana da abun da yake son cimma, kawai kayan ne gaba ɗaya ba sa ɗaukarsa gaba ɗaya yanzu, ka san yana cikin matsananciyar damuwa, duk kayan cajin nan kansa ba ya ɗauka kamar aljani, amma ina bincikawa, an yi mini alƙawarin wata zazzafar ƙwaya, daga kudu suke kawota. Yanzu dai wannan aikin da ya ce , maza-maza ka kira kwangila a waya, ya haɗa mana yara, a basu kayan caji, zamu fasa ƙofa, ai Madaki shi da ɗaukar wata fansa a kanmu, sai dai a lahira idan ana yi. Sai mun ga abun da ya turewa buzu naɗi. Ɗan mama ya miƙe ya ce "Ok, bari na hanzarta na fara haɗo su ta arear wajen garin nan". Walid ya ce "Nima fitar zan yi, wurin liti zani, zan shiga karɓar balance". Suka fice gaba ɗaya. Bayan tafiyar su Aminu ya koma cikin ɗakin, ya fara duba in da walid yake ajiye ƙwayoyi, amma ya dudduba bai gansu ba, ya zazzage ko ina, amma babu. Wani irin takaici ya tokare masa ƙirji, ya ja dogon tsaki, ya ɗaga gefen katifarsa, allurar sa saura kwalba biyu kawai, kuma ya san ba ɗaukarsa za ta yi ba. Haka ya zuƙe ta ya yi wa kansa, sai dai kamar kullum, yau ma ƙirjinsa ne ya fara da zafi, kansa yana juya masa. Wuƙar da take gefensa yake ta kallo, zuciyarsa na raya masa abubuwa daban-daban. Tun da Ramma ta suka isa cikin kano, gidan da take aikatau, kayanta kawai ta sauke a ɗakinta, ta hau aikace-aikace. Duk da akwai wata mai aikin, wadda ta girmewa ramma, sosai da sosai, amma matar gidan ita ta yarjewa ta shiga sashenta, har uwar ɗaka da na maigidan ta gyara mata, a cewarta ramma ta fi nutsuwa, kuma ba ta taɓa ƴar aikin da ba ta yi mata sata ba, sai ita. Matar gidan da ƴaƴanta gaba ɗaya sun tafi dubai hutu, shiyasa ta sallame ta, ta ce ta je gida ta huta, za su yi wata biyu kafin su dawo, kuma kwatsam yanzu sati biyu wai dawowa za su yi. Tana falon matar gidan, tana ta uban aiki, ɗan kwanakin da aka yi ba a taɓa wurin ba, duk ya yi ƙura. Ƙofar falon aka shigo, ta tashi da sauri, tana kallon mai shigowar, dan ba ta yi tsammanin ganin kowa a sashen ba, dai-dai wannan lokacin. *** Nabila kuwa kusan kwanaki uku curr, ta kasa nutsuwa da kwanciyar hankali, da ta kwanta bacci, sai mafarkin karnuka, tayi ta ihu. Haka Anty da baba magajiya za su danneta, su yi ta shafa mata man gelo da miski, ta ja bakinta, ta yi shiru, ba ta gaya musu abun da ta aikata ba. Yau kuwa gajiya ta yi da zaman gidan, dan baka cikin hijjabi ta shirya, ta ɗauki ƴar ƙaramar wayarta, ta fito falo. Umma ta kalleta ta ce "Ke da baki da lafiya, ina zaki je kuma?" Nabila ta ce "Wurin aiki, akwai buƙatar in je zan kai wani bayani ne mai muhimmanci" "Amma kin gaya masa, kar ya dawo ya tarar kin fita, ya yi ta faɗa" "Umma ba daɗewa zan yi ba" Saudat ta ce "Mhmm, a ma faɗi gaskiya, ko yawon banza za aje". Nabila har za ta yi shiru, ta ga idan tayi shiru, za ta cutu, dan haka ta ce "Idan fitsari banza ne, kaza ma tayi, idan yawon ma zan tafi, mai lasisi ne akwai riba, ke ki yi mana" Umma ta kalli Sauda ta ce "Sauda dan Allah ki din ga jan girmanki, Nabila fa ba sa'arki ba ce ba". "Na saka da ke ne?" Umma ta girgiza kai ta ce "A'a baki saka da ni ba, Allah ya taimaka". Sumayya tana ta aiki a news room, Nabila ta yi sallama ta shiga. Sumayya ta kalleta ta ce "Ina aikin?" "Ban je ba, ya aikin?" "Lafiya ƙalau, meyasa ba ki je ba?" Nabila ta ce "Ke ba wannan ba, yanzu na ga managern ku a waje muka gaisa" Sumayya ta ce "Good, ya aka yi?" "Rahotonki na last week, a kan case ɗin yarinyar nan da aka yi wa fyaɗe, na ji shiru baku sake cewa komai ba" Sumayya ta ce "Eh ya aka yi?" Nabila ta ce "ina da intrest a kai ne, ina son shiga lamarin, na ji shiru haryanzu babu wani update, na an ɗauki mataki" Sumayya ta ce "Dalla ware, kamar wata lawyer kirki, you are not even serious about the job" Nabila ta ce "Ke ban son wulaƙanci fa, am serious, na ji an ce wanda yayi laifin mai lasisi ne a garin nan, ina son sanin waye shi?" Sumayya ta ce "Nima ban sani ba" "Kamar yaya ba ki sani ba, am serious fa, da gaske nake sumayya ina son shiga case ɗin, free of charge na taimaka wa yarinyar, na ji tausayin su sosai da sosai, yadda uwar take kuka. Kuma daga ji ƴan karkara ne, masu ƙaramin ƙarfi". Sumayya ta galla mata harara ta ce "Sannu ambulance uwar taimako, manyan lawyoyi sun riga sun shiga case ɗin tuni, sai ki ja gefe" "Suwaye manyan lawyoyin? Kuma wai waye dan Allah, waye yayi fyaɗen?" "Ke! Nifa a rubuce aka bani, karantawa kawai na yi, hatta recording ɗin da aka saka, na muryar uwar da ƴar, tararwa na yi an yi, ban ma gansu ba, ban ga suwaye ba, balle na samu wani bayani. Case ma fa lamarin ya kusa zama a gidan nan, saboda saka muryar matar da aka yi, murtala ne dama ya yi recording ɗin ya saka, sai da aka kusa korarsu" Nabila ta ce "To fa, ina murtalan yake?" Sumayya ta ce "Ba zan nuna ba, kin ganki Nabila" "Ba wani abu zan yi ba, sonake kawai ya haɗani da matar da yarinyar". "Babu fa abun da zaki iya yi a kai, shi ma bai san waye wanda yayi fyaɗen ba, yarinyar aiki take a gidan, baƙo ne daga zuwa yayi mata. Dan Allah ki haƙura da case ɗin nan" A ɗan fusace ta ce "Saboda me?" Sumayya ta yi murmushi ta ce "Na ji an ce mutuniyar ki da jama'arta sun shiga cikin case ɗin, shiyasa na ce ki haƙura" Nabila ta ce "Wa kenan?" "Naja bunkure mana, antynki mudubinki, a bar ƙaunarki" Sumayya ta yi maganar tana dariya. A take annurin fuskar Nabila ya ɗauke, haka kurum jikinta ya bata babu gaskiya a lamarin nan. "Uban mudubin nawa, in dai wannan mudubin ne, Allah ya fasa shi na huta, wallahi sumayya tun daga abun da matar nan ta yi mini, kawai nake ji a jikina fuska biyu ce da ita, wadda take kallon jama'a da ita, da kuma wadda take ɓoyewa" "To ko ma dai yaya ne, sun shiga case ɗin, kin san kuma ba zasu tsaya su saurareki ba, mussaman da ta iya yi miki kallon ke ba komai ba ce ba" Nabila ta ce "Haka ne, amma rai dai an cire wa fara kai, lokaci ne, yana nan zuwa da zan bawa duniya mamaki, sai na saka ƙafa na bi ta kanta ko da halin ƙaƙa" "To ki bi a hankali, kar ke duniyar ta baki mamaki" Nabila ta yi shiru tana tunani. Sumayya ta ce "Ya dai?" Tayi guntun tsaki ta ce "Sumy zaman gidanmu babu daɗi, kamar in gudu wallahi". "Wai Nabila ba zaki daina wannan iƙirarin ba?" Ta girgiza kai ta ce "Ba zaki gane ba, faɗa muka yi da Siyama, har da Abba ayi mini faɗa, sauƙinta ɗaya ta ci duka da tukunya na din ga dukanta" "Haba Nabila, wannan ai yawa ne, degree holder da dambe?" "To yaya ki ke so in yi? In zuba mata ido ta yi mini duka? Ga uwarsu ta addabi rayuwata, ba ta san yadda ta tsane ni, nima haka na tsaneta ba, kawaici kawai nake yi mata ba. Duk uban ƴan matan gidan nan har da zaurawa, babu wanda duka sanyawa ido sai ni, da na motsa ayi ta janyo mini jafa'in karuwanci" ta ƙarasa maganar hawaye na cika mata ido. Sumayya ta ce "No dear, dan Allah ki ƙara jurewa, lokaci ne da kin yi aure zai wuce" "Yaushe zan yi auren? Dan Allah ni mummuna ce Sumy? Duk saurayin da ya zo, sai za a fara maganar aure, sai ya gudu kamar wata jaɓa" "Nabila kina da matsala, Babu wata halittar Ubangiji mummuna. Ga ki fara, ga gayu da ilimin addini da na zamani, kina da kwarjinin da ki ke bawa maza tsoro ne, ai ke kalar manya ce tawan, ba duk kai ba" Cikin takaici Nabila ta ce "Ba wasu manya, manyan da suka din ga yaudarata Allah ya isa da ba su aure ni ba suka ɓata mini lokaci, ni yanzu kowaye ma zan aura na bar musu gidan, ko ba na son shi. Idan ba haka ba wallahi wataran sai na gudu" Sumayya ga tausayin Nabila ga dariya, tabbas Nabila akwai farijinin samari, masu kashe mata kuɗi ma kuwa, sai dai Nabila ta fiye zaɓe-zaɓe, kuma ba ta fiye ba wa masu sonta da gaskiya muhimmanci ba. "Ki gudu ki je gidan uban wa? Gaki ga Abba nan maza ki gudu kar ki fasa" Sai kuma ta koma rarrashinta, har bayan azahar suna tare, sai da sumayya ta tashi suka fito tare. A reception suka tarar da wani mutum, ana ta yi masa fadanci, yana hura hanci cikin manyan kaya na alfarma, reception ɗin ko ina security. Sumayya ta risuna ta gaishe shi ya amsa, amma Nabila ko kallonsa ba ta yi ba, ta sunkuyar da kai, kamar alla-alla take yi, ta yi ta bar reception ɗin. Ɗan rikicewa yayi, ya ƙura mata ido, amma ta basar ba ta gaishe shi ba, sai so yake yi ta ɗago su haɗa ido, dan ya tabattar da abun da yake tunani, amma taƙi ta mayar da kanta gefe. Mamaki ya shiga yi, yana tunanin ko dai gizo idonsa yake yi masa? Sai dai ya rasa abun yi kafin ya yi wani yinƙuri, sun bar reception ɗin. Ɗaya daga cikin ma'aikatan ya kalla ya ce "Wannan mai hijjabin ma'aikaciyar ku ce ita ma?" Ya girgiza kai ya ce "A'a sir, she's just a guest here" Ya ce "She looks familiar to me, anyway shikenan dai" yayi gaba. Cike da takaici Sumayya ta ce "Kina kallon babban mutum ki ka basar ba ki gaishe shi ba, sai kallonki yake yi, ki ka sani ko shi ne mijin a dace a daidaita ko ƙyasawa yayi? Da irin wannan halin naki, ki ke korar samarinki na kirki wallahi". "Kin fi kowa sanin bani da baƙin hali, wasu lokutan ma cewa ki ke yi na fiye zaƙewa" "Haka ne, amma baki kyauta ba, ko dan kallon da yake yi miki, ai kya kula shi". Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Ban taɓa jin na tsani wata halitta a kallon farko da na yi mata a rayuwata ba, sai wannan mutumin. Gaba ɗaya ya canza mini mood lokaci guda" Sumayya ta waro ido ta ce "Meyasa kun taɓa haɗuwa ne? Me yayi miki?" "No, ina ganin shi a poster dai, ba ɗan majalisa bane? Ban taɓa jin komai idan na ganshi a poster ba, sai yau da na ganshi ido da ido, bana fatan Allah ya sa na sake sanya shi a idona. Kin san me? ji nake kamar ya taɓa cutar da ni, cuta mai muni" "Arfa, kina hayyacinki kuwa? Tayaya mutumin da ki ka fara gani yau kawai, ki ce kin tsane shi, ya cutar da ke how?" "Ban san tayaya ba, amma haka nake ji a raina, kuma da gaske nake jin hakan" "Ki daina irin wannan wasan, kar ki saka a din ga yi miki mummunar fassara" "Forget, ba zaki gane ba" tayi maganar a daidai lokacin da suka ƙaraso titi. Tun ba ayi sallar magariba ba, walid ya riga ya gama tatara gayyar matasa zauna gari banza, wanda suka yi bankwana da fatan samun ingantacciyar rayuwa, suka kama makamai da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi. Kasancewar ba a cikakken hankalinsu suke ba, haka suka raraka kowa da kowa gida. Yaran madaki, na ta shirin shiga ɗaya unguwar sare-saren ɗaukar fansa. Labari ya iske su cewar, yaran Aminu sun rigasu yin dirar mikiya. Ba su yi zaton gayya guda, yaran aminun suka ɗaukko ba, dan haka suka fita domin su far musu. Kamar ba jikin ɗan Adam ba, haka suka din ga sara da sukar junansu, mutanen unguwa duk suka shiga gida suka rufe. Aka yi rashin sa'a madaki baya nan, ɗaya daga cikin yaransa, ya kira shi ya sanar da shi halin da ake ciki. Nasir yana zaune ya idar da sallar magariba yana lazumi, so yake ya tambayi ina arfa, ya ga ya jikinta, amma mama na babban falo, ya san da ya yi hakan, za ta yi masa faɗa, tare da sake gargaɗinsa a kan Nabila. Wayarsa ce ta fara ringing, ya shafa addu'ar, ya ɗaga tare da yin sallama. Da sauri ya tashi tsaye, yana faɗin gashi nan zuwa. Da sauri ya ɗauki mukullin motarsa, ya fito daga sashin mama, zuwa falo. Mama ta kalleshi ta ce "Ya dai? Ya na ganka a birkice?" Dai-dai lokacin Nabila ta fito daga ɓangaren ɗakinsu, hannunta riƙe da kofi, hakan ya sanya ya kasa ba ta amsa. Zuciyar sa ta tsananta bugawa da sauri, doguwar rigar material ce a jikinta, kanta babu ɗankwali, tayi parking ɗin gashinta. Wani irin kyau ta ƙara yi masa. "DSP yaushe ka dawo?" Tayi maganar tana kallonsa. "Da magaribar nan, yanzu nake shirin nemanki, in ga ya jikin naki? Wayarki ba ta shiga" Anty ta ce "Jiki yayi kyau, har fita tayi" "Fita kuma, ki ka je ina? Kuma da iznin wa?" "Dan ubanka ina yi maka magana ka shareni, maganarta ta fi tawa muhimmanci ne ko yaya?" A ɗan rikice ya ce "A'a mama, yi haƙuri kiran gaggawa aka yi mini, faɗan daba ya ƙara ɓarkewa, ƴan daba sun rufe unguwar babu shiga babu fita, yaran Aminu Viper ne da wani madaki, wai ƴan sandan da aka tura, sun kasa kwantar da rigimar, kin san am incharge of his case, shi ne zan je na ga abun yi" "To ka kula da kyau, ni wannan aikin ya isheni, shikenan kai ba hutu, ni hankali a tashe". Ya jinjina kai ya nufi ƙofar fita. Jin an ambaci Aminu, ya sanya jikin Nabila ya hau tsuma, ya bishi da gudu ta riƙo rigarsa ta ce "DSP, amma ba kai kaɗai zaka je ba ko?" "Eh, na yi waya za a ƙaro mini ƴan sanda" "Ko mu je tare?" Ya zaro ido ya ce "Ki yi me?" Sai kuma ta rasa me za ta ce "Kawai dai ko zan iya taimakawa" Murmushi ya yi ya ce "Ba fa kotu ba ce madam" "Zaki sake shi ya tafi ko kuwa? Wane irin iskanci ne haka, Meye haka ne Nasir?" Nabila ta saki rigarsa ta ɗan ɗaga murya ta ce "Take care, ka tsaya daga nesa nesa dan Allah, kar wani abu ya same ka, kar mu yi asarar ɗan ƙasa na gari" Dariya ya yi, ya fita da sauri. Mama ta hayyayaƙo mata "Wallahi ki kiyayeni da rashin tarbiyyar ki a kan ɗa na, na gaya miki" mama ta yi maganar tana nuna Nabila da yatsa. Nabila a ranta ta ce 'Ni yanzu ba ke ce a gabana ba, akwai abubuwan da suka fiki muhimmanci a wurina" Tayi gaba tana kiran lambar sumayya, ta sanar mata da halin da ake ciki, na rikicin faɗan daba. Sai dai kamar kullum, faɗa suka yi, sumayya ta gargaɗeta a kan ta fita sabgar harkar faɗan daban nan. Nabila tayi zuciya ta kashe wayarta, tare da jin da ita ƴar jarida ce, sai ta shiga unguwar nan, ta samo rahoto, tana matuƙar jin haushin yadda sumayya take ɗari-ɗari da gudanar da aikinta, sai dai ko ba dan sumayya ba,  ya zama dole ta taimakawa Nasir, kuma ta taimaki tata career, dan idan ba ta rama abun da Najar bunkure tayi mata ba, ba zata huce ba dan haka za ta cigaba da bibiya. Ayshercool 08081012143 [7/23, 1:37 PM] null:                                     *ƘARFE A WUTA* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Follow this link, to join autar manya channel, domin samun litattafanta na baya da na yanzu. https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h Masu neman book ɗin ƘARFE A WUTA daga farko, su bi wannan link ɗin, su yi following channel ɗin, za su samu previous pages👇👇👇. https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g 9 Har ƙarfe goma na dare, Nabila tana kiran wayar Nasir, domin jin ko yana lafiya, amma shiru wayarsa ba ta shiga, abu kamar wasa hankalinta ya fara tashi, zuciyarta ta din ga raya mata wani abun ya same shi. Da sauri ta tashi ta fita farfajiyar gidan, tana cigaba da kiran wayarsa. "Ke Arfa, me ki ke yi a wurin nan da daddare haka?" Ta ji muryar Abba babu tsammani. Cikin damuwa ta ce "Abba Yaya bai dawo ba, kiransa aka yi kwantar da tarzomar faɗan daba, kuma haryanzu bai dawo ba". Abba ya ce "Yana nan lafiya in sha Allah, da ki ka dawo nan kina sintiri,ai ba bin sa zaki yi ki nemo shi ba, harkar aiki ne yana nan lafiya in sha Allah" Abba yana rufe bakinsa, sai ga ƙarar motar Nasir, yana ta horn ba ƙaƙƙaitawa, gaba ɗaya suka nufi gate a tare. Suka tsaye har ya shigo yayi parking ɗin motar. Ya fito yana kallon su da mamaki ya ce "Abba lafiya na ganku a nan tsaye?" Major ya ce "Arfa ce ta fito tana jiran dawowarka, ya ya aka yi wayarka ba ta shiga gaba ɗaya?" "Tana cikin mota ne abba, ina ga network ne amma a kunne take" Cikin zaƙuwa ta ce "Yaya, komai lafiya dai ko?" Ya ce "Alhamdilillah, an sha artabu dai, yaran sun ninka yawan da muke tunani, mun kama wasu, wasu sun gudu, amma mun kama su da yawa". Mama ce ta fito ita ma, tare da su sauda, suna yi masa sannu da zuwa yana amsawa. Arfa ta ce "Amma dai ba su yi maka rauni ba ko?" Yayi murmushi ya ce "Da sun yi mini rauni, ai da baki ganni a haka ba" Nabila ta ce "To Alhamdilillah, bari na je na kwanta na yi bacci a nutse, tun da kana lafiya" Ya ce "Ki bar wayarki a kunne, za mu yi magana" Ta jinjina masa kai ta bar su a wurin ta tafi, mama kuwa kamar ta bi Nabila ta naɗa mata duka, ta kalli yadda Nasir yake wani sassanyan murmushi kamar shashasha, shi ma ji ta yi kamar ta kwaɗe shi da mari, duk ƙoƙarin da take yi a kansa na nesanta shi da Nabila, abu ya ci tura. Ta daure ta ce "Shiga ciki ka ci abinci, ka je ka nemi wuri ka kwanta". "No na tsaya na ci abinci a hanya ma, sai da safe, gajiye nake kwanciya zan yi" Major ya ce "To Allah ya tashemu lafiya" suka watse. A galabaice suka koma mafakarsu, domin kuwa sun sha artabu da jami'an tsaro, duk da an kama wasu, wasu kuma sun tsira da ƙyar. Sai dai sun yi wa su madaki mummunar ɓarna, dan ma Aminu ya yi musu kashedin babu ruwansu da cewa za su kashe madaki, saboda ya san hatsabibancinsa. Yana zaune suka faɗo ɗakin, suna ta mayar da numfashi, jikin rigar ɗan mama face-face da jini. Walid ya ce "Boss, an yi aika-aika amma kwaɓarmu ta so yin ruwa, dan an kama da yawa daga cikin yaran nan da muka gayyato, amma fa yaran madaki sun yi ɓarna, dan sun taɓa wanda ba su ji ba, ba su gani ba, duk da mun yi yinƙurin daƙile hakan". Maimakon Al'amin ya yi magana, kawai ya tashi tsaye ya shaƙo wuyan walid, ya haɗa shi da bango, ya ware masa idanunsa ya ce "Ina ƙwayoyin da ka kwashe a nan wurin?" Cikin takaici walid ya ce "In fita yi maka aiki, in dawo da ƙyar amma ka shaƙe ni?" Yayi maganar muryarsa na fita da ƙyar saboda shaƙar da ya yi masa. "Suna ina na ce?" "Na kwashe su na fita da su, dan ba zan bari ka kashe kanka ba, allurar da ka ke yi wa kanka ma, ba abun da take yi maka sai ƙara maka zafin zuciya" Fusata yayi da maganar Walid, ya ƙara shaƙe shi, Ɗan mama ya tashi da sauri yana yi wa Al'amin magiyar ya rabu da Walid. Walid ya ce "Idan ka kashe ni ma, ba zaka huce ba, ai na yi maka alƙawarin kawo maka sabuwar ƙwaya, amma wannan kashe kanka zaka yi, idan ka cigaba da sha, dan ba ta karɓe ka ba." A fusace ya hankaɗe Walid ƙasa, ya koma ya zauna ya dafe goshinsa. Wayarsa ce ta yi haske, ya ja wayar yana dubawa. "Aminu ka daina wannan gangancin da ka ke yi, idan ka sake shiga hannun mutanen nan, kar ka yi zaton za su hukuntaka da adalci, dai-dai da abun da doka ta tanada, ka nutsu ka daina wannan mugun wasan, ka mayar da hankalinka a kan burinka" iya ƙarfin sa ya saka wurin yin jifa da wayar, ta dagargaje a tsakiyar ɗakin, ya tashi zai fita. Duk da mugun ciwon da jikin walid yake yi masa, saboda artabun da suka yi, amma haka ya tashi ya sha gaban Al'amin ya ce "Ina zaka je ne?" Hankaɗe Walid yake ƙoƙarin yi, amma walid ya sanya ƙarfin sa, ya tura shi baya. "Ka rabu da ni walid, ya zan yi ne? So suke sai na haukace, waye wannan? Me yake nema da rayuwata? Wace manufarsa ce da su a kaina? Me kuma suke buƙata yanzu?" "Easy master" Cikin ƙaraji ya ce "Na ce kar ka sake kirana da wannan sunan" "Sorry boss, na san komai ai, ka kwantar da hankalinka" "How? Duk abun da suka yi mini bai ishe su ba, wai yaya zan yi ne? Kalli idona walid, ba na bacci fa, zuciyata kullum zafi take yi, ba na iya saka komai a bakina na ji ɗanɗanonsa,  ya zan yi ne?" Walid ya ce na sani, ya amsa yana yi wa ɗan mama inkiya da idonsa. Viper ya a sake cewa "Ka san kwana nawa na shafe ba na bacci? Ba kwanaki ban ba fa kawai, shekaru ne, ba na baccin da ya kai awanni biyar, ka san me nake ji kuwa?" Walid ya ce "Ban sani ba, amma na san da yawa daga abubuwan da ka lissafa" Jikinsa na tsuma ya ce "Wallahi zuciyata ci take yi da wuta, ka sani, wallahi idan na riƙe makami sai na yi kisan kai" yayi maganar yana rintse idanunsa, a lokacin da ruwan allurar da walid yake yi masa, ya fara ratsa jijiyoyin jikinsa. A nan take jikinsa ya saki, ya zubawa walid ido. Walid ya ce "Ko ba zaka yi baccin ba, ka rufe idanunka master, za ka samu releif" shiru yayi, domin ba zai iya motsa kowacce gaɓa daga jikinsa ba. Ɗan mama ya ce "Walid, anya ba zamu yi wani abu a kan lamarin nan ba kuwa? Ba za a kai shi ya ga likita ba? Kar ya haukace tuburan fa" Walid ya ɗora yatsansa a kan laɓɓansa alamar ɗan mama ya yi shiru. A hankali al'amin yake buɗe idonsa yana lumshewa, sai dai ya kasa ƙwaƙwƙwaran motsi. *** YALOKO ƘARAMAR HUKUMAR TOFA. Cikin tsananin ƙyanƙyami take ƙarewa ɗan ƙaramin ginin ƙasar kallo, rabin katangar gidan  ta zube, sai ciko aka yi da kara da buhu, aka rurrufeta. Abunka da mutumin ƙauye, cikin mutunci da girmamawa, matar gidan ta karɓeta, tana yi mata sannu da zuwa. Ta yi mata iso, har cikin ɗakinta, ta ba ta abun zama. Kamar ta zauna a kan kashi, haka ta ɗan ɗosana ta zauna, tana kame jikinta ta kalli matar ta ce "Baki gane ni ba ko?" Matar ta ce "Eh ban waye ki ba" "Ni ce barrister da na karɓi case ɗin ƴar ki, na zo mu tattauna ne, in yi magana da ita" Nan da nan hawaye ya cika idon matar ta ce "Tana banɗaki, bari ta fito" rufe bakinta ke da wuya, yarinyar tayi sallama a ɗakinta, muryarta ƙasa-ƙasa. Mahaifiyarta ta amsa, barrister kuwa zuba mata ido ta yi, yadda yarinyar take ɗingishi, take tafiya da ƙyar, har ta zo ta zauna. Ta kalli uwar ta ce "Kun kaita Asibiti ne?" Ta ce "A'a, tun dai a  can an kaita, maigadin gidan ne ya kaita, har aka yi mata ɗinki a goshinta, gashi nan in da aka ya ji mata rauni. Dan Allah baiwar Allah ki taimake mu, kamar yadda Allah ya taimake ki, a karɓar wa yarinyar nan hakkinta. Saura ƴan kwanaki aurenta, ya lalata mata rayuwa, idan zancen nan ya fasu a garin nan yaya zan yi?" Ta kalli yarinyar sannan ta kalli uwar ta ce "Baiwar Allah kuma hadda halinku, na son abun duniya duk yadda hukumomi ke jan kunne a kan kai yara aikatau meyasa ba kwa ji? Meyasa zaki kaita aikatau, maimakon makaranta?, a ƙa'ida fa kema sai an hukunta ki" Cikin rauni da damuwa ta ce "Baiwar Allah da ina da yadda zan yi yaushe zan kaita aikatau? An yi garkuwa da mahaifinta an ce mu kai kuɗin fansa, mun tattara dabbobi da gonaki mun sayar, mun bayar a kai a sako shi, sun rike ƙanin mahaifinta da ya kai kuɗin, sun haɗa su su duka sun kashe, gona ɗaya ta rage mana, ita ma wani mutum duk ya tarkata ya ƙwace, wai zai gina kamfani, an ce za a bamu diyya, gonar miliyan uku an bani dubu bakwai, abun da zan girka na basu su ci, ita da ƴan uwanta, bani da shi, nima ba cikakkiyar lafiya ce da ni ba, kuma ita ce babba, makaranta tana zuwa ajinta uku a sakandare, kuɗin da ake biya na makarantar ba ni da su, ya zan yi?" Tayi maganar kuka yana ƙwace mata. "Shikenan ya isa haka?, Amma kuma irin haka kin yi gaggawa zuwa gidan radiyo ki faɗa, ai wurin jami'an tsaro yakamata ki je". Maman ramma ta ce "Na je, dan da aka kira ni na je can birnin asibiti, da ƙyar aka karɓe ta wai ba ɗan sanda, daga can na je wurin ƴan sanda naga suna nema su cuce ni, wai ƙarya muke yi, babu yadda za ayi a ɗauki ƴa ta aiki a wannan gidan har ayi mata fyaɗe. Ba ki ga sintirin da na yi ba, na rasa abun yi shiyasa na kai wurin masu radiyo ko Allah zai saka a taimake mu" Ta jinjina kai ta kalli yarinyar ta ce "Ramma  ko?" Ta jinjina kai alamar eh. "Gaya mini yaya aka yi abun ya faru?" Ta ɗaga kai ta kalli mahaifiyarta, sai ta fashe da kuka ta kasa magana. "Hajiya ɗan bamu wuri mu yi magana" babu musu, ta tashi ta fita ta bar ɗakin. "Kin ga ki yi shiru ki kwantar da hankalinki, ki yi mini bayanin yadda abun ya faru, in ga ta ina zamu ɓullowa lamarin" Shiru ta yi tana tuna yadda lamarin ya kasance. "Ke!" Ya kirata cikin tsawa, bayan sun haɗa ido da ya shigo, ƙara razana ta yi, dan ba ta yi zaton wani zai shigo yanzu ba, a dai-dai wannan lokacin, da ta duƙufa tana ta aiki a falon gidan. cikin tsuma ta kalleshi ta ce "Na'am". "Ina masu gidan?" Yayi maganar yana ƙare mata kallo, matashiyar yarinya ce, da ba ta wuce shekara goma sha huɗu ba, irin farkon tashen balagar nan, ƙirjinta ya fara tasawa, wannan ne karo na biyu da yake ganinta a gidan. Tun a ranar farko yake jin wani abu na fuzgar shi a kanta. Cikin rawar murya  ta ce "Ai ba su dawo ba tukuna, gyaran gidan dai muke yi". "Ke kaɗaice a gidan kenan?" Cikin rashin wayo ta ce "Eh, amma zulai ta je sayo katin waya, zata dawo, tare muke aiki da ita, wai a satin nan za su dawo". Yayi wata irin ajiyar zuciya ya ce "Ɗaukko mini ruwa a kitchen zan sha" ta jinjina kai, ta ajiye duster hannunta, ta tafi da sauri har da gudu. Sai dai tana shiga kitchen ɗin, ya bi bayanta, ya mayar da ƙofa ya rufe. Turus ta tsaya tana kallonsa, jikinta yana rawa, taga ya fara tunkaro ta. Ta ja da baya ta miƙa masa ruwan, amma ya haɗa da hannunta ya riƙe. "Dan Allah ka sakeni, in ƙarasa aikina" Babu tausayi ko imani, ya ce "Nawa aikin zaki fara yi tukuna, kafin nata" Ganin akwai alamun ƙarfi a tare da ita, ba zata tsaya ba, ya sanya ya gaura mata wani lafiyayyen mari. A take hancinta ya fara zubar da jini. Ta ƙwala ihu, ya sake buga kanta da cabinet na kitchen, goshinta ya fashe, nan ma jini ya hau zuba, ga goshi ga hanci, dan haka ta kasa magana, jikinta ya saki. Haka ya keta mata haddi, ta hanya mai muni da rashin tausayi ya tashi ya fice ya barta. Idonta biyu, amma ta kasa taɓuka komai, ko ɗaga hannunta ta kasa yi. Zulai ce ta dawo ta tarar da ita cikin mummunan yanayi, a rikice ta fita ta kira ɗaya daga cikin masu gadin gidan, suka ɗauke ta suka kaita Asibiti. Aka ƙi karɓar su, sai da aka kira matar gidan aka sanar mata, suka yi magana da likitoci ta waya. Sai dai duk abun nan, ramma ba ta san ko sunansa ba, balle ta san ɗan waye shi. Kafin matar gidan ta dawo, ta aiko a bawa ramma kuɗi, a bata haƙuri su koma ƙauye, ko warkewa ba ta yi ba aka sallame su, shi ne mamanta ta ɗauke ta suka tafi gidan radiyo. Ramma ta bawa barrister labarin komai, tana kuka mai taɓa zuciya, goshinta ga ɗinkin da aka yi mata a asibiti, ga na ƙasanta da yake addabarta da raɗaɗi. Tayi ajiyar zuciya ta ce wa mahaifiyar ramma ta shigo. Bayan ta shigo ta zauna, ta kalle su ta ce "Baiwar Allah, dan cuta na san an cutar da ku, amma za ki sake jefa kanki a halaka, gara ku yarda ayi masalaha. Babu wata kotu, ko wani alƙali, da zai tsaya miki ya ƙwato muku hakkinku, saboda yaron nan ɗan gata ne gaba da baya, ubansa suke da ƙasar. Dan haka ki yi haƙuri, a baku wani abun, ki samu ku sai abinci, a kuma kaita asibiti, idan ta warware ta koma makaranta. A take ramma ta fashe da kuka, mahaifiyarta ta ce "Haba baiwar Allah, shikenan bawa dan talaka ne, ba zai samu adalci ba, kuɗi zasu ƙare, mutuncin ƴa ta fa? ni gaskiya so nake a karɓa mata hakkinta". Barrister tayi shiru tana zancen zuci "Ko yaushe mutumin ƙauye ya wani san ƴancinsa? Da matar nan take zaƙewa?' "Naira miliyan uku za a baku, kuɗi hannu, ki yi tunani zan sake dawowa. Idan kuma kun ƙi, zan cire hannuna, duk matakin da uban yaron ya ɗauka a kanku babu ruwana, ina sake gargaɗinki, babu ke babu magana da wani ɗan jarida ko makamancin haka, idan kunne ya ji jiki ya tsira" ta ciro kuɗi a jakarta, ta ajiye musu, ta tashi ta fice. *** Kamar zai tashi sama, saboda tsananin tashin takaici da haushi, ya ce "Madaki, wace irin shiririta ce wannan ku ka yi, ta yaya zaku bari, jami'an tsaro su sake kamaku?" Cikin muryarsa da ta riga ta fashe irin ta mashaya ya ce "Kai ka san ba laifinmu ba ne ba, wani banzan bakware aka kawo mana, kai zaka tsawatar, ka saka a sake su, dan idan babu su babu aikin nan" "Shikenan, na ji, ka saurare ni da kyau, zuwa hankali ya riga ya kwanta, mutane sun manta da abun da ya faru watan baya, ina son a cigaba da yi mini aikina, amma a wannan karon yankin yamma da gari zaku je, yaron kar ya wuce ɗan shekaru goma zuwa sha biyar, jininsa nake buƙata, a zuba a babban dam ɗin da yake rarraba ruwa a yankina, tun daga mazaɓata, sai ku kawo mini ƴan marainan yaron, da hanjinsa. Sa'ar aikin ranar laraba ce bayan al'muru. Idan kujerata ta cigaba da tabattuwa kuma zaku mora" Madaki ya ce "Wannan ba zai yi wahala ba, ka huta kawai, kujerar nan ko an so ko an ƙi, mai hawanta sai bayan ka mutu honorable" "Eh, amma ba yanzu zan mutun ba ai, sai an kwana biyu tukuna, zan aiko maka kuɗi, ayi abun da yakamata larabar tsakiyar wata za ayi, yaranka kuma za a sake su" "Sai da kai honorable, ka ci dubu sai ceto" "Yauwa yayi". Nabila kuwa sannu aka din ga yi mata a wurin aiki, ana tambayarta yaya jiki, ta din ga amsa musu da yauwwa. Ofishin barrister Habib ta je, ta gaya masa yadda suka yi da matar, da duk abun da ta yi documenting. Ya karɓa ya duba sannan ya kalleta ya ce "Yayi, amma me ki ke gani a kan case ɗin? Do you have interest on it?" Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Wani case na jiyo, na wata yarinya da aka yi wa fyaɗe,amma ana ta ɓoye abun, amma na ji an ce su barrister Naja'atu sun shiga case ɗin, hankalina ya fi karkata a can". "Wai ke menene haɗinki da wannan naja'atun ne? Ki kiyayi kanki da lamarin matar nan,tun da sun shiga case ɗin, ki ƙyale su, case ɗin wannan hajiyar ki tsaya ki mayar da hankali a kai ki yi" Ta marairaice ta ce "Amma barrister menene aibun hakan, tun da class mate ɗin ka ce, ka haɗa ni da ita dan Allah, ina son irin aikace-aikacenta na jin ƙai" Ya cire medical glass ɗin sa ya kalleta ya ce "Wai ke meyasa ki ke da taurin kai ne? Ke ma ki kafa naki harkar jin ƙan marasa gatan mana, dole sai kin zama ita, ke kin san wacece Naja'atu kuwa? Zahirinta ki ka sani, baki san baɗininta ba, go and work on this case now". Tsatstsare fuskar Barrister ta yi da kallo, a ranta ta ce "An zo gaɓar da nake so, hasashena ya tabbata, zan cigaba da matsa ka, har sai ka amayar da abun da ka ke ɓoye mini" A fusace ya ce "Ba zaki tashi ba, ki ka tsare ni da ido?" Miƙewa tayi tana zumɓura baki, ta ɗauki file ɗin ta fice. *** Kaiwa yake ta yi yana komowa, a katafaren office ɗin sa, hannunsa riƙe da waya a kunnesa, yana jiran a ɗauka. Har fitar da ran za a ɗauka, aka ɗaga. Cikin harshen turanci ya ce "Haba sir, kai fa nake jira kayan nan su iso, almost 2weeks, ayi ta ga kaya nan amma shiru, ni na riga na gama clearing road, a yankinmu na arewa, ka hanzarta na fara jin ƙishin-ƙishin canjin controllers na coustom, bana son a kawo waɗanda za mu yi ta fama" Daga cikin wayar mutumin ya ce"Sai fa ka yi haƙuri, kayan ne ba a gama loda su ba, kuma nima dole sai na gama da controllers ɗinmu na nan, kuma ka daina ɗaga hankalinka, babu wani wanda ya isa a ƙasar nan, ya sha abun da ba mu muka dama ba, ranar laraba kaya za su shigo, amma sample ce allurar, ba a shigo da ita da yawa ba, sai an ga yanayin aikinta tukuna, har da tablet ma" "To na ji, amma ka tabattar ranar larabar za su iso?" "Ko tantama babu" "To shikenan, godiya nake"ya katse wayar, cikin shauƙin irin ribar da zai mayar idan kayan suka tsira. Zaune take a ƙasaitaccen ɗakin baccinta, jikinta sanye da riga da wando na nylon, masu sauƙin zafi. Ta zauna ta nutsu, ta zubawa kayan kan table ɗin gabanta ido, tana ta saƙe-saƙe a kan ta sha ko kuma kar ta sha. Kwalabe ne na magunguna, da ƙwayoyi haɗi da allurai. Wata matashiyar mace ce tayi sallama, ta amsa mata, ta ƙaraso hannunta riƙe da cup ta na shan wani abu. "Sweetheart, ya dai na ga kin saka kayan nan a gaba kina kallo?" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Tunani nake yi da zuciyata, in sha ko kar in sha" "So you are going to quit abusing drugs?" Ta girgiza kai ta ce "Is not that easy dear, jikina is resisting it, ba sa ɗauka ta sai na sha su in a very high doses, ba na son su huda ni, a fara ganewa. Mun yi magana da honorable a kan sabuwar allurar da suka yi order daga Mexico yana ta yi mini yawo da hankali" "Haba barrister, ke fa ta hannun daman honorable ce, ba zai yi miki yawo da hankali ba. An samu wani zazzafan malami fa" Ta ɗago idanunta ta kalleta ta ce "Wow, are you serious?" "Yes of course, aikinsa tested and trusted ne, amma kafin muje a kan buƙatarki, anya ba zaki duba a manyan mutanen nan, mu kai wani ba, ki yi aure yadda zai zama backup kar abubuwa su zo su taɓarɓare fa, ko ki samu wani kamar tsohon mijinki, ki aura" Ta taɓe baki ta ce "Ba zan iya aure ba, na riga na saba da rayuwar ƴanci, ba zan yi aure in zauna ƙarƙashin wani yana juya ni yadda yake so ba. Ai tun da na yi joining organization ɗin nan kin san in da na dosa". Ta ce "Na sani dear, amma duk da haka, religion da tradition yana da tasiri sosai da sosai a arewacin najeriya, ba na son wani ya gano wani lagonki, ayi amfani da shi wurin yaƙarki" Ta girgiza kai ta ce "Muddin ba zan samu wanda zan gindayawa sharuɗa ya bi ba, zan iya zamana a haka, i have so many ways to satisfy my feelings, when i need it, ba dai duk su ake yi wa a auren ba? Kin san komai ai ke. Ki saka mana time, mu je wurin mutumin, ba na son sunana ya ɓace, har sai na cika burina, na kammala aikin da na karɓo a wurin shugabannina, sai na tabattar da samun daidaituwar jinsi a tsakanin mutanenmu na arewa" Badi'a ta yi dariya ta ce "Ki huta baby, ki ɗan yi caji, sai ki kwanta, ko in fita da ke ne?" "No, ba na son na yi bacci da yawa, zan sake komawa wurin matar nan, a kan case ɗin ɗan gidan honorable, naga alamar za ta yi taurin kai, idan taƙi yadda kawai mu bi hanyar da muka saba bi" "Hmm, talaka akwai ƙi faɗi, kuɗin ne ba zata karɓa ba kenan? Sa yi biyu babu kuwa" "Manta da su, idan ki yi waya da journalist ɗin nan, manta sunasa nake yi, ki tura masa kuɗi, a cigaba da ɓoye wanda ya yi laifin, a sanarwa da duniya na shiga case ɗin, a sassaka a social media ma, a dai yi ƙoƙarin ɗauke hankalin mutane daga kai" ta ƙarasa maganar tana tuttula ruwan maganin da ke cikin wata ƙatuwar kwalba tana lumshe ido. Yau Abba kamar ya san Nabila so take ta lallaɓa ta fita, ya zauna a gida bai fita ko ina ba. Tayi iya tunanin ƙaryar da zata sharara masa, ta fita amma ta kasa tunawa, dan idan ya tsitiyeta zai gane ƙarya take yi, gashi weekends ne babu aiki. Cikin ikon Allah, aka samu tarzomar su madaki da Viper ta ɗan lafa, saboda an jibge jami'an tsaro a unguwannin. Nabila har alla-alla take yi, ranar Monday tayi ta fita aiki, daga nan ta tafi nata wuri. Ranar Litinin tun sassafe wasu daga cikin iyaye mata, suka fara sintirin karɓar belin ƴaƴan su da aka kama, a ofishin su DSP Nasir. Nasir yana zuwa ya tarar da su, an ce musu su jira sai ya zo. Tsakanin iyaye da ƴaƴa sai Allah, amma wannan rashin juriyar yana ɗaya daga abun da yake taka rawa, wurin sake sangarta yaran. Bayan sun gaisa da su, ya ce "Da farko ina mai baku haƙuri, domin kuwa ba za mu bayar da belin yaran nan ba, sai mun kai su gaban alƙali tukuna. Yaran nan ku kanku sun fi ƙarfin ku, ba kwa iya tsawatar musu, suna barazana ga zaman lafiyar al'umma, dan haka ku yi haƙuri a wannan karon babu sabo babu ɗaga ƙafa, sai dai na yi muku alƙawarin duk wanda muka kama ba shi da laifi, zamu sake shi, masu laifi kwai zamu kai gaban hukuma". Bai tsaya jin mai zasu ce ba, ya wuce office ɗin sa. Koke-koke wasu daga cikinsu suka fara, yayin da wasu suka din ga janyo masa jafa'i kala-kala, wai an zalunce su, an rufe musu ƴaƴa. A cikin office ɗin sa ya karya, kasancewar ya makara, bayan ya kammala, ya je in da ake tsare da yaran, tare da taimakon wasu daga cikin jami'an tsaro, ya fara tuhumar su, da ƙoƙarin zurfafa bincike akan su gaya masa in da viper yake. Wanda aka ritsa ɗin ana tuhuma ya ce "Wallahi Yallaɓai, da ne dai kafin ya je prison, na san in da yake, har gidansu na sani, muna yi masa aiki sosai da sosai, amma tun da ya fito bamu sake ganinsa ba, su Walid da tarago ne suka san in da yake, tarago kuma madaki ya kashe shi, walid kuma wallahi shima ba a ganinsa, muna yi masa aiki amma bamu san in da yake ba". Nasir ya ce "Ta yaya ku ke karɓar order daga wurinsa?" "Randomly, suke zaɓar mutum ɗaya su kai masa takarda, ko aje a ajiye takardar a in da muke taruwa shikenan" Nasir zai sake magana, wayarsa ta fara ruri, ya zura hannu a aljihunsa ya ɗaukkota, ya ɗaga ya saka a kunne, tare da yin sallama. "Kana ina ne?" "Na shiga wurin aiki sir" "Yaran nan da ka kama, ka sake su, kowa ya tafi, kuma ka janye jami'an tsaron da ka jibge a unguwar" cikin tsananin mamaki ya tashi tsaye ya ce "Sir, yarane da suke ɓarna fa, har kisan kai aka yi a ranar, yaya zamu.... "This is an order from higher up Nasir, ka saki yaran nan, nima umarni aka bani daga sama, Aminu Viper muka ce ka kamo mana, ba yaran unguwa ba" Ya taune lips ɗin sa na ƙasa cikin ɗacin rai ya ce "Amma sir, muna kan binciken wanda suka yi kisan kan ne". "Ka sake su nace, is an order" Nasir ya ce "Ok sir, as you wish"ya kashe wayarsa, jikinsa yana wata irin tsuma, ya tuna yadda a garin kamo yaran, sai da suka kusa kashe shi, a artabun da suka yi, ga kisan kai, ga miyagun makamai da suka kama yaran da su, amma an bashi order ya sake su, anya kuwa ana son kawo gyara da matsalar tsaro a ƙasar nan!? Ƙarfe a wuta paid book ne, few pages zan bayar free, masu buƙata za su iya contacting ɗi na, su fara subscribing, miƙaƙƙiyar tafiya ce, mai cike da sarƙaƙiya da ban al'ajabi. Ayshercool 08081012143 [7/24, 1:44 PM] null: *ƘARFE A WUTA* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Ku yi following channel ɗin nan, domin samun littatafan autar manya. https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h Masu son ƙarfe a wuta daga farko, ku bi link ɗin nan ku yi joining channel ɗin https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g 10 Gaba ɗaya zuciyarsa ta cunkushe, ya rasa me ma Yakamata yayi. Ya daɗe a zaune kafin ya tashi ya fita reception ɗin. Sai dai yana zuwa ya tarar da wani mutum a tsaye, baƙi ƙirin da shi, ya ɗaura ɗan kwali a kansa, ga wasu wulaƙantattun kaya a jikinsa kamar mahaukaci, idanuwansa jawur kamar an rina masa. Nasir ya ce "Lafiya kuwa? Wannan fa?" Ya dube shi ya ce "Kai ne Nasir ko?" Yayi maganar yana shagiɗe kafaɗa irin na cikakkun mashaya. Nasir ya ce "Ya aka yi?". "Na san ka samu saƙon ka sakar mini yarana, na zo na tafi da su ne" Wani irin ƙululun takaici ya tokare zuciyar Nasir, yayi ajiyar zuciya ya ce "Kai ne wa?". Yayi wani irin ihu, ya jinjina kai ya ce "Madaki nake, gumbar dutse, na san ko bamu yi gaba da gaba da kai ba, ka san labarina, ina son wannan ya zama gargaɗina da kai na farko na ƙarshe, babu kai babu shiga harkata da yarana, idan ba haka ba" Nasir ya tsare shi da ido, ban da lalacewa ace ɗan ta'adda ne zai shigo har office yana yi wa jami'in tsaro kashedi, saboda wasu masu faɗa a ji sun tsaya masa. Yayi murmushi mai ciwo ya ce sergent Iliya, ka fito da yaran nan gaba ɗayansu" Ya amsa masa da "Ok sir" Nasir ya zagaya, ya kama gefen rigar madaki, suka fita waje, ya kalle shi ya ce "Wanene Aminu? Ina zan same shi?" Madaki ya ce "Wane Aminun?" "Viper, na san ka san shi, tun da an ce abokin rigimarka ne" Madaki ya buɗe wawaken bakinsa, da wiwi duk ta dafar da haƙoran, laɓaɓansa sun zama manya, sun yi baƙi saboda taba, ya kwashe da dariya ya ce "Tabbas! Na san shi, ɗan zaki ne, da na yi sake ya girma yake neman gagarar kundila, dan da na kashe shi tun a wancan shekarun da haka ba ta faru ba. Nima neman sa nake yi ruwa a jallo, ko a raye ko a mace, dan haka idan ka same shi, ka sadani da shi. Sai dai ka bi a hankali wurin neman sa, jami'anku su suka masa sunan Viper, kumurci ne mai hatsari da idan ya sareka zai kashe ka" A dai-dai lokacin matasan suka fito harabar station ɗin suna ihu, suna sarawa madaki, wasu daga cikinsu kuma da ba yaran madaki bane ba suka fice. Nasir ba ya tunanin tun da ya fara aiki, ya taɓa cin karo da abun da ya ɓata masa rai kamar wannan, sai ya ji gaba ɗaya aikin ya fita daga kansa. Haka ya ja tawagar matasan suka bar harabar station ɗin suna iface-iface. Duk yadda Nabila ta so ta samu damar guduwa, daga wurin aiki yau, ta kasa samun dama, dan haka ba ta tashi ba sai ƙarfe uku, a lokacin ba ta da wani kuzarin kirki, babu abun da take buƙata wanda ya wuce ta tafi gida. Ba ta fi mintuna ashirin da shiga gida ba, Nasir ya dawo. Bayan sallar la'asar ya kirata a waya, ya ce ta fito yana son ganinta. Ba ta ɗauki lokaci ba, ta fita harabar gidan, wajen parking space akwai fararen kujeru. A can ta tarar da shi, sai dai yanayinsa ya tabbatar mata akwai damuwa "DSP, yana ga kamar ranka a ɓace ne?" Tayi maganar tana zama. "Damuwa kam akwaita, gagaruma kuwa arfa" Ta girgiza kai ta ce "Subhanallah, meyafaru yayana?" Nasir ya ce "An saki yaran nan fa, da muka kama shekaranjiya" Ta waro ido ta ce "Saboda me?" Ya ɗan ɗage kafaɗa ya ce "Saboda yaran ƴan siyasa ne, ina zuwa office aka kira ni daga sama, wai suma umarni aka yi musu, kar in sake kama yaran, aikin neman Aminu aka saka ni ba wannan ba, na daɗe ba ayi mini abun da ya ɓata mini rai irin wannan ba, kamar ni wai ni ɗan daba ya kalleni a cikin kakina, yake yi mini kashedi a office could you imagine. Sai an yi magana ace ba ma taɓuka komai, an janye jami'an tsaron da aka ajiye a unguwar ma" Nabila ta daki tebur tana huci, zuciyarta har wani tafasa take yi ta ce. "Shikenan, da wanda suka kashe, da kwanciyar hankalin mutanen unguwar, duk ba matsalar su ba ce ba? Personal interest ɗin su ne kawai a gabansu?" "Gashi kuwa kina gani, yanzu idan na matsa zasu iya raba ni da state ɗin nan ma gaba ɗaya, ni kuma bana son barin garin nan saboda, i don't want to miss you dear" Kamar za ta yi kuka ta ce "Wallahi Yaya gaba ɗaya aiki ya fita daga kaina, anya ba haƙura zan yi na kama kasuwanci ba, kai babu daɗi, sumayya ma haka, nima dan jan wuya ce, idan aka addaba mini ajiye aikin zan yi, gaba ɗaya ayyukanmu na taimako ne, amma ɓata gari sun yi kane-kane a ciki. Yanzu menene abun yi?" Nasir ya ce "Abun yi kawai na mayar da hankali, na yi musu abun da suka ce, shi kansa wanda suke son a kama ɗin, ina zargin wani abu ne akansa, ko tsakaninsa da wani ya sanya suke son in kama shi, ban da baka ya za ayi ace ɗan daba ya gagara kamuwa, alhalin yana cikin garin nan" Ta ce "To ka ce ba zaka yi ba mana, idan sun matsu su manyan su kama shi mana" Yayi dariya cikin takaici ya ce "Ba zai yiwu ba arfa" Ta kwantar da murya ta ce "Ka kwantar da hankalinka yaya, komai lokaci ne, sai dai duk ranar da Allah ya sa muka kai wani matsayi, mu yi iya yinmu, wurin ganin ana tsage gaskiya duk ɗacinta, lokaci ne ka yi haƙuri" Yayi murmushi ya ce "Idan ban yi haƙuri ba, ya zan yi, dolena ai, na san lokaci ne Ta ce "Yauwwa, in sha Allah, da ni da kai da sumy, zamu yi nasara a rayuwar aiki, and zan yi duk iya yi na, na ga ka kama aminu" Nasir yayi murmushi ya ce "How? Na yi amfani da techniques ɗina, na kama masu laifi, amma na kasa samunsa, akwai alamun shi ma yana da masu tsaya masa" "Mu ma Allah ya tsaya mana, zamu yi yaƙi da duk wani mai kawo cikas ga aiki da adalci" Dariya ta bawa Nasir ya ce "Ka ga ƴan ƙasa nagari" suka yi dariya gaba ɗaya. *** Sanye yake da gajeren wando, da riga armless baƙa, joint ne mai kyau sosai da sosai, yanayin matasan da suke shiga suna fita, zai tabattar da na masu hannu da shuni ne. Ya ɗora ƙafarsa a kan kujera, yana ta shan shisha, kusa da shi wasu matasan ne, suma suna ta nasu shaye-shayen. Sai matashi ɗaya da yake kujerar da take facing ɗin sa, yana shan sigari, ya kalli Abdul ya ce "Kai Abdul, wai wannan lumshe idon da ka ke yi, lafiya kuwa?" Ya sauke ƙafafuwan sa, ya tashi ya gyara zamansa ya yi wani murmushi ya ce "Ba lafiya ba" yayi maganar yana murmushi. "Ba lafiya ba kuma ka ke dariya?" Ya girgiza kai cike da shauƙi ya ce "Na rasa ya zan yi ne, tun ranar da na samu wata cika, under 18, na sarara na kasa mantawa da ita, duk matan da nake harkata da su, na kasa samun abun da nake so, kamar yadda na samu a wurinta. Ashe duk wahalar banza nake yi da nake biyewa manyan yaran nan" Saif ya ce "To ka koma mata mana" Abdul ya ce "I rape her" yayi maganar yana sake sakin hayaƙi a iska. "Rape kuma? How?" Abdul ya ce "I don't know, i was drunk, bai gama sakina ba kuma, na je gidan aunt maijidda, na tarar da yarinyar ashe ba ta gari ita da mijinta, duk yadda nake da ƙyanƙyami, nake son manyan mata, amma na kwaɗaitu da yarinyar nan, tun a ranar farko da na fara ganinta. I don't know why, but i still need her, na kasa samun yadda nake so, ita ɗin dai nake son sake kasancewa da ita. Warin da jikinta yake yi, make me more crazy on her, she was the first under 18 virgin i mate, i don't think... Saif ya katse shi ta hanyar cewa "Anya kana hayyacinka kuwa? Ko ka sha wani abun ne bai sake ka ba, ka ke yi mana surutun banza, ka yi raping ɗin under 18 old girl, kana vewa warin jikinta make you more crazy are you well?" Abdul ya gyara zamansa ya ce "Saif da gaske nake, i rape her, dad is even working on it, mamanta wai har sun shiga media sun kai ƙara. I don't care what so ever, i still need her, at any cost". "Abdul, ka ce dad ɗinka yana ƙoƙarin a rufe case ɗin, amma kana wannan zancen, ka san idan magana ta shiga media sai a hankali, da kai da dad ɗin abokan hamayya za su saka ku gaba". "Abu nawa na yi babu wanda ya fashe? I don't care, you will help me in nemo yarinyar nan, na ji dad ya ce naja ta shiga case ɗin, kuma ba wata ba ce ba, she's just maid da gani ka san yar talakawa ce" Cikin tsoro, Saif ya waro ido ya ce "Wannan barrister? Aikuwa ka kaɗe Abdul, an ya zaka sha wannan karon?" Abdul ya kwashe da dariya, har sai da ya janyo hankalin wasu kansu ya ce "You don't get sense, malam zaka taimake ni na sake nemo yarinyar nan, itakaɗai ce maganin ƙishirwata" yayi maganar yana cigaba da ƙyaƙyata dariya. *** Abun da Nasir ya gaya wa Nabila, ya ƙara azalzalar ta, akan son samun Viper, ta tabbatar da kama Viper zai iya zama silar cigabansa da ɗaukakar da take nema. Sai dai ta kawar da tunanin daga zuciyarta, a lokacin da ta nutsa, tana kallon hotunan Barrister Naja'atu a social media. Ayyukanta na jin ƙai, da makamantansu. Babu wani information da zai gaya mata haƙiƙanin wacece Naja'atu Bunkure, amma ta barwa zuciyarta lallai akwai wani abu a ƙasa a kan ta, kuma zata tono shi. Ranar talata da safe tana shirin fita aiki, sumayya ta kirata ta ce su haɗu, a in da suke saba haɗuwa, su tafi tare. Tun da Nabila ta ji haka, ta san akwai wani abu a ƙasa, dan haka ta amsa mata da to. *** Walid ne yake ta yi wa Al'amin lissafi, da bayanin ayyukan da ya saka ayi masa, amma sam hankalinsa baya kan abun da walid ɗin yake faɗa. "Viper" walid ya kira shi. Maimakon ya amsa sai ya ce "Haryanzu babu wani labari a kan masu zuwa gidan malam lawan?" Walid ya numfasa ya ce "Babu" Ya ce "Yaran nan gaba ɗaya aka sake su, tare da yaran madaki ko?" "Eh, ɗazu duk suka fita, an sake su duka". Yayi ajiyar zuciya ya ce "Zuciyata tana bani, kamar so ake a ɗauke hankalina daga abun da na ƙuduri aniyar yi, ni kuma wallahi muddin ina numfashi a doron duniya, sai dai ayi mutuwar kasko" "Amma tayaya haka zai yiwu, alhalin ka kasa sakin jikinka ka ɗauki ƙaddara, ba ka cin abinci, baka walwala, daga kwanciya, sai shaye-shaye, sai bayar da umarni, yakamata ka sakawa zuciyarka salama" "Walid!" Ya ambaci sunansa da ƙarfi. Ya amsa masa da "Viper" "Tashi ka fita" Cikin mamaki ya kalli Viper ya ce "In fita kuma? Ni ɗin walid ne fa?" "Eh ka tashi ka fita ka bani wuri" "Saboda ina bibiyarka, ina yi maka biyayya ka ke neman ka wulaƙanta ni? Ban da darajar ni ɗan halak ne da ba na manta alkhairi, kai ka san da tuni na daɗe da barinka" Aminu ya ce "Idan kai ɗan halak ne, a wannan karon ina son ka bar ni" Ya sake kallon viper ya ce "Ni ka ke kora?" "Eh bana buƙatar sake ganinka" Walid ya jinjina kai ya ce "Ok, na fahimta" ya tashi tsam, bai sake cewa komai ba ya fita. Aminu ya nemi wuri ya kifa kansa, ya dafe saitin ƙirjinsa. "Ni zaku mayar tamkar ƙwallon ƙafa, ku din ga bugani a tsakanin ƙafafuwan ku? Kun yi kuskure" ya furta cikin sanyin jiki. *** Tun da suka haɗu, sumayya na tsuma ta fara bawa Nabila labari. "Arfa kin san menene?" "Faɗi kar ta kashe ki" "Wannan satin, Honorable Ma'aruf indabo, zai yi program a gidan rediyon mu, kuma ni manager ya ce zan yi hirar da shi" Nabila ta yi murmushi ta ce "Wow congrats baby" Sumayya ta ce "Nabila, ba abun congratulations bane, indabo fa, wanda kwanaki aka ci mini mutunci a kansa, da na je mazaɓarsa ban tarar da ayyukan da aka ce yayi ba, shi ki ka gani a reception fa, da baki gaishe shi ɗin nan ba". Nabila ta ɗan waro ido ta ce  "Aikuwa sai ki rama, ki zaƙulo masa tambayoyi na tsitsiyewa, tambayar yaya uwarka ta haifeka, ke har waccan maganar ma ki ɗaukko, ki tutsuye ɗan bantan uba, ƴan siyasar nan wasu babu Allah a ran su" Ta ce "I wish ina da wannan damar, sai dai program ɗin ba live bane ba, kuma wai rubuto mini tambayoyin da zan yi masa za ayi mini, kamar dai karantawa zan din ga yi yana bani amsa" "Ban gane ba, interview zaku yi, ko kuma tattaunawa a kan cigaban da ya kaiwa mazaɓarsa?". Sumayya ta ce "Bari kawai nabila, dama murtala ne yake program ɗin, kuma baya nan aka ce na yi, ina ta murna amma gwiwata tayi sanyi, kuɗi ya biya sosai za ayi program ɗin, amma a ɓoye campaign kawai zai yi, kin san zaɓe ya fara ƙaratowa" Nabila ta ce "Taɓ abun tsiya, toshi da ƙosan rogo, wannan kawai tambaya da amsa zaku yi, haka yaya Nasir yazo yana gaya mini wai ƴan daban da ya kama, an kira shi daga sama wai ya sake su, abun babu daɗin ji, naga alamar sai mun zama jan wuya mun zage a kan ayyukanmu, yanzu dai ki ƙarasa, zamu yi waya zan shiga wata unguwa, muna da client zan duba wata shaida ne" Sumayya ta ce "To shikenan, mu yi waya ko kuma ni sai in zo gida" "Ok bye" ta tsayar da mai adaidaita sahun ya tsaya ta sauka. Wata adaidaita sahun ta tsayar ta hau, ta tafi unguwar ƙofar na'isa. Shagon nan da ta taɓa tsayawa ta sai lemo, nan ta tafi. Cikin mutuntawa, mai shagon ya karɓeta suka gaisa, da yake ya gane ta  ya ce "Hajjaju kin dawo unguwar ta mu kenan?" Ta ce "Eh malam, da wata alfarma na zo nema ne" Ya tattara hankalinsa a kanta ya ce "Ok, ina jin ki" Ta ce "Last da na zo, wannan mutumin da na tarar a nan, na ce masa ya taimaka mini ina son na haɗu da aminu Viper, amma ya kwatanta mini wani wuri, wai lungun iraƙi, suka kusa kasheni" Mai shagon ya zare ido ya ce "Viper kuma? Ke menene haɗinki da shi?" "Ɗan uwana ne, tun da ya fito daga prison, ban sake ganinsa ba" Ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Allah ya rufa miki asiri da ba su kashe ki ba, kin san yadda suke nemansa ruwa a jallo kuwa? Idan suka riga jami'an tsaro kama shi, kashe shi za su yi. Kuma a iya sanina, babu wata mace da Viper yake da alaƙa da ita, dan haka ki rufawa kanki asiri, ko sunansa kar ki fiye ambata a cikin unguwar nan" Nabila ta waiwaya bayanta, babu kowa a wurin, ta ɗebo kuɗi ta ajiye masa ta ce "Waye shi, ko a taƙaice ne ka gaya mini wanene shi, a ina zan same shi" "Ki ka ce ɗan uwanki ne?" "Ka manta kawai, ni dai ka taimaka mini" Yayi ajiyar zuciya sannan ya ce "Hajiya, na tabatta kina da alaƙa da hukuma, gaskiya ina jin tsoro, ina da iyaye da ƙanne, da nake taimakawa, ko basu saka an kashe ni ba, sai an yi mini illa, muddin na gaya miki wani abu, daga baya su gano ni na faɗa" Nabila ta ce "Manta da batun hukuma, ba ni da alaƙa da ita, kuma babu yadda za ayi na bar wata ƙofa da zata nuna ka gaya mini wani abu, taimakona zaka yi, idan kuɗin sun yi kaɗan zan ƙara maka wallahi". Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Aminu sun taɓa zama a unguwar nan, bayan ya zama ɗan daba na iraƙi ake ce masa ko kuma mai dogon zamani, ƴan sanda ne suka saka masa Viper, saboda rashin tsoronsa, da azabar kwarjinin da yake da shi, gagararre ne sosai, kuma dealer ne na miyagun ƙwayoyi. Kuma matasan yaran nan marasa ji, suna jin maganarsa fiye da ta iyayensu, ba zan iya gaya miki sama da haka ba, amma zan kwatanta miki, in da zaki samu wani yaronsa, amma dan girman Allah, kar ki bari sunana ya fito, ki taimaka" Nabila ta ce "Na yi maka alƙawarin babu wanda zai ji". Ya ce "Idan magariba ta yi, ki je tal'udu, hannunki na hagu, akwai wanda yake zuwa a kan babur ya zauna yana sayar da katin waya, ya saka facemask. Ba katin yake sayarwa ba, balance yake karɓa na yaran da suke rarrabawa tabar wiwi, ƙananan dealolin su, da suke yi sayar musu da katan maye, yaron Viper ne makusantansa ne sosai, amma dan Allah ki riƙe alƙawari". Nabila tayi ajiyar zuciya ta ce "Zan riƙe in sha Allah, na gode sosai". Ta sake ƙara masa kuɗi. Fita daga shagon, tana jin kamar ta riski fiye da rabin matsalarta, idan Allah ya sa ta yi wa DSP hanyar kama aminu, atleast ta taimaka masa. Babu tsoro ko tunanin komai, ta ƙallafawa ranta ko ta halin ƙaƙa za ta yi nasara. Honorable Ma'aruf indabo, yana kashingiɗe a katafaren falon sa, hannunsa riƙe da waya ya kara ta a kunnensa, yana jiran a ɗaga. Muryar madaki ce ya amsa da "Sai mai gida" Indabo ya numfasa ya ce "An sakar maka yaran?" "An sake su mai gida" "Yayi kyau, ka fara ƙoƙarin yi mini aikina, zan shiga Abuja wannan satin, ka tabattar aikin nan ya kammala kan na dawo" "Baka da matsala oga" "Yauwwa, ya batun Aminu?" Madaki ya ce "Wallahi duk wata kafa da za a bi wurin samunsu, ya tsosheta, jiya wani ɗan sanda yake tambayata wai idan na san in da yake" Da sauri indabo ya tashi zaune ya ce "Waye shi? Meyasa yake tambayarka?" "Wallahi ban sani ba, amma dai shi ne ya kama mini yara, Nasir mai tama na gani a jikin kakinsa" Indabo ya jinjina kai ya ce "Shikenan zan bincika" Wata mata ce ta buɗe ƙofar ɗakin, ta shigo, hannunta riƙe da ƙaramin plate ɗauke da tuffa, ta ƙaraso kusa da shi ta zauna. "Ya dai na ganka kamar a tsorace?" Indabo ya ce "Madaki ne ya ce mini wai wani ɗan sanda yana tambayarsa Aminu jiya, dole na saka a bincika waye". Cikin takaici ta kalleshi ta ce "Au da kanka ka ke waya da ɗan daba, abun da ya faru tsakaninka da Aminu bai zame maka izina da darasi ba, kana ganin yadda ya zame mana barazana, ɗan tahaliki ɗaya ya hanaka sukuni". Ya ce "Na san abun da nake yi bilikisu, komai a lissafe nake yin sa, ai na yi kuskure na farko, ba zan yi na biyu ba. Aminu kuma ina da tabbacin akwai wani abu a ƙasa, kuma zan kawar da shi, kafin ya buɗe bakinsa". Ta ajiye trayn hannunta ta ce "Yanzu ya ake ciki da maganar Abdul, haryanzu Naja'atu ba ta ce komai ba?" "Nima ita nake saurare, na fiki damuwa ma da wannan lamarin, amma dole ki ja masa kunne, na fara gajiya da rashin mutuncin sa, ba zai ɓata mini siyasata a banza ba, ina ta fafatuka a kai, ya je ya yi abun da ƴan adawa zasu samu abun faɗa a kai ba". Ɓata fuska ta yi ta ce "Kai ma ɗanka ne ai, ka ɗauki matakin da ya dace da shi" ta ƙarasa maganar ta tashi ta bar masa ɗakin. Yayi guntun tsaki, ya ɗauki wayarsa yana kiran wata lamba. "Honorable, Allah ya taimake ka" "P.A ya turo muku list ɗin tambayoyin da zaku yi mini ko?" "Eh ya turo, mun kuma bawa mai gabatarwar da ka buƙata ta dudduba" Ya jinjina kai ya ce "Ina fatan yarinyar da na ce maka ce?" "Eh ita ce Yallaɓai" Ya ce "Yayi khau, ku turota gidana, ta zo ta yi recording ɗin a nan, ba zan samu zuwa nan ayi program ɗin ba" Cikin damuwa manager ya ce "Ina fatan ba wani laifin ta sake yi ba ranka ya daɗe?" Indabo ya ce "Da zan hukuntata, tun laifin da ta yi mini na farko, da tuni na hukunta ta, wani abu mai muhimmancin gaske na gani a tare da ita, da nake son tabattarwa" "Subhanallah, dan Allah yallaɓai ka yi haƙuri, idan laifi ta yi, ina nema mata afuwa ". "Jamilu, ka turo yarinyar nan gidana, tayi recoding ɗin program, kar ka sake yi mini musu". Ya kashe wayar ya ajiye. Yanayin yadda zuciyarta ke tsananta bugawa ne, ya sanya ta din ga karanto duk addu'ar da ta zo bakinta. Sai dai ba ta ji za ta iya janye aikata abun da tayi niyya ba. Nesa kaɗan da in ya kwatanta mata ta je ta tsaya, sai dai tun kafin duhun magariba ya gama rufawa, mutumin da aka kwatanta mata ya zo ya kafa teburinsa na sayar da katin waya, ya nemi wuri ya zauna. Ta ɗan jima a tsaye, tana kallon sa, sannu a hankali ta fara tunkarar in da yake zaunen, tana addu'a a zuciyarta har ta ƙarasa in da yake. Kafin ta yi magana, wani matashi ya rigata ƙarasawa, suka gaisa ya miƙa kuɗi, aka bashi wata baƙar leda. Ta tattaro jarumtarta ta yi sallama ta ce "Sannu malam" ya ɗaga kai ya kalleta, sai dai kamar ya razana da ganinta. Ta sake cewa "Sannu malam" "Yauwwa" ya amsa da kakkausar muryar sa, yana cigaba da ƙare mata kallo. "Dan Allah kaya nake so" ya ƙare mata kallo daga sama har ƙasa, ya ce "Wane irin kaya?" "Irin wanda ka ke sayarwa, amma ni direct nake son na din ga karɓa" "Jami'ar tsaro ce ke?" Yayi maganar yana cigaba da kallonta Nabila ta ce "Jami'an tsaron ai sun san da zamanka a nan, ina so ka haɗa ni da Aminu viper ne" Waro ido yayi ya kalleta ya ce "Ke! Yayi maganar yana zazzaro mata ido" Tayi ƙasa da murya ta ce "Kar ka ɗaga murya, ka taimaka mini, ɗan uwana ne, tun da ya fito daga prison ban sake ganinsa ba" "Ƙarya ki ke yi wallahi! Ban da ke mace ce, da namiji ce ke, wallahi sai na ciro hanjinki waje na zubar a titi, bar wurin nan, kafin na karya ki" Nabila ta marairaice ta ce "Ba ka da tabbacin ƙary..... "Ki bar nan, kafin na tsarga ki biyu da makami" ta ja da baya a hankali, tana kallon sa. "Ki bar nan na ce" ta juya da ɗan sauri, cikin tsoron yadda ya hayayyaƙo mata. Wayarsa ya ɗaukko ya kira Walid yana huci, cikin sa'a ya ɗaga. Walid ya ce "Maza ya ne?" "Wata yarinya ta zo neman boss, wai ƴar uwassa ce, anya ba a fara bibiyar sa ba? Idan ba haka ba, yaya aka yi ta san na sanshi". Cikin mamaki walid ya ce "Kar dai yarinyar da gagare ya ce mini ta je dabar madaki neman sa?" "Ban sani ba, amma zan so ka ganta, ka ga wani abun mamaki, mai ɗaure kai, dan na kusa guduwa wallahi" Walid ya ce "Kamar yaya?" "Ka ga, ina hangota haryanzu, zan bita na yi mata magana, zan ce ta dawo gobe da safe, zaka ga abun da na gani" Walid ya ce "Kai liti, ka tabatta ba matsala?" "Babu, kawai sonake ka ganta" "Shikenan, idan ka tashi yau, ka shiga area wurin dila, ya baka balance, idan na zo zan karɓa" "Sai da kai, an gama" Nabila na shirin hawa ɗan sahu, ta ji an yi fito a bayanta, ta waiwaya ta ga liti a tsaye. "Zo mana" yayi maganar yana kallonta. Kawai zuciyarta ta raya mata, ko wuƙa zai soka mata. "Ki zo mana" yayi maganar cikin tsawa. Cikin rauni ta ce "Dan Allah ba wuƙa zaka soka mini ba?" Ya ce "Ke da kashe ki zan yi, kin isa na bari ki bar wurin nan, shawara na canza, ban san alaƙar ki da shi ba, dan haka zan haɗa ku" Da sauri ta ɗan ƙarasa gabansa ta ce "Dan Allah, amma na ji daɗi na gode sosai da sosai". "Mu haɗu a nan, gobe ƙarfe biyar na yamma, zan haɗaki da wanda ya san in da yake, amma wallahi ki ka yi wani abu na rashin gaskiya, kin san sauran" Nabila ta ce "Babu wani abu na rashin gaskiya da zan yi, na gode yayana Allah ya saka da alkhairi" Ya ce "Ke ki nemawa kanki tsari, da na zama yayanki, ware ki bar nan" Hamadala ta yi, tare da jin kamar wata gagarumar nasara tana tunkarota. Ƙwas-ƙwas takalminta yake bayar da sauti a kan tiles ɗin wurin, sai sauri-sauri take yi ta ƙarasa ofishin manager. Da sallama ta shiga, ya ɗago ya amsa mata, ta ɗan risuna ta ce "Afuwan sir, na tsaya ƙarasa editing ɗin news ne, shiyasa ban zo kiranka da wuri ba". "Bakomai sumayya, sannu da ƙoƙari, ina yabawa ƙoƙarin ki da himmarki". Tayi murmushi ta ce "Na gode sir" "Ina sisternki, young barrister ne? Nabila ko, kwana biyu ba ta kawo mana ziyara ba" Sumayya ta yi murmushi ta ce "Ayyuka ne suka yi mata yawa, amma ko ɗazu muna tare" Ya ce "To Allah ya taimaka, yauwwa dama batun program ɗin nan ne, honorable ya ce ba zai samu zuwa ba, sai dai aje can gidansa ayi recording program ɗin, dan haka driver zai kai ki, a can badawa gidansa yake, za a kai ki ranar Friday, sunday zai yi tafiya ki yi recording program ɗin" Cikin mamaki da sanyin jiki, ta ce "Gidansa kuma sir? Amma ai yau murtala za su dawo, tun da su maza ne sai su je.... Ya ɗaga mata hannu ya ce "Look sumayya, ya zama dole ki je, murtala ba zai dawo yau ba, honorable ba wani abun zai yi miki ba, gidan da yake zaune da iyalansa ne, recording ɗin program kawai zaku yi. Idan kuma ba zaki yi ba, you know the consequences" Wata irin nannauyar ajiyar zuciya ta yi, ta ce "Allah ya kaimu" ta juya a hankali ta fice. ₦500 ne, via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank Special wanda ba sa son group 1k. Wanda za su jira document, idan an kammala 1k ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa wannan layin Sai a tura mini shaidar biya ta 08081012143 ko 07063065680 Ayshercool 08081012143 [7/25, 1:18 PM] null: *ƘARFE A WUTA* AREWABOOKS: ayshercool7724 Watpad: ayshercool7724 What's app: 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g 11 Bayanta manager ya bi da kallo, ta bashi tausayi sosai da sosai, sai dai yana addu'a Allah ya sa kar honorable ya cutar da ita. Kamar ɓarawo, haka walid ya diro a tsakar gidan, maimakon ya biyo ta ƙofa, ɗan mama yana zaune yana shan sigari a ɗan tsakar gidan. Bai kula shi ba, ya wuce ɗakin da viper yake, sai dai ya duba baya ciki. Walid ya dawo, ya kalli ɗan mama ya ce "Ina Viper?" Ɗan mama yayi dariya ya ce "Har ka gama fushin, ka dawo?" Walid ya ce "Kai ka san ba zan iya ba, ƙular da ni yayi ne, ina yi masa uzuri ne kawai na san kansa ya taɓu, yana ina?" "Baya nan" ɗan mama ya bashi amsa kai tsaye. "Kamar yaya? Ina yaje?" Ɗan mama ya zuƙi sigarinsa sannan ya ce "Ni na isa na hana shi fita ne? Ko kuma na ce sai ya gaya mini in da za shi? Da dai kai ne zai iya ɗaga maka ƙafa" A fusace walid ya ce "Dan me zaka bari ya fita?" "Au so ka ke na hana shi, ya karya ni, ko ya illata ni, kaɗaici ne ya dame shi, gidan babu kayan caji, sai na hayaƙi, shi ne ya fice. Yauwwa dama ina son gaya maka, ka daina kwashe kayan cajin nan gaba ɗaya, idan wani yayi rawa an bashi kuɗi, kai idan ka yi, na jaki zaka ci a hannunsa wallahi" Cikin takaici Walid ya ce "Wai so ka ke sai ya kashe kansa ne? Kana kallon allurar nan ba ta ɗaukar sa, farar ƙwaya ma fa ba ta yi masa komai, sai rikita masa ƙwaƙwalwa, idan ya haukace fa?" Walid gani yayi ɗan mama yayi tsuru-tsuru, yana rarraba ido, dan haka ya waiwaya bayansa, Al'amin ya gani a tsaye a bayansa. Bai kula su ba, ya zo ya raɓa walid ya wuce. "Master"ya kira shi. Al'amin ya waiwayo, fuskarsa babu annuri, idanunsa sun yi ja, jijiyoyin kansa suka miƙe ya ce "Me na ce maka a kan kirana da haka?" Walid ya ƙarasa kusa da shi, dai-dai kunnensa, ya yi masa raɗa. Viper ya kalli Walid ya ce "Kasheni ka ke so ka yi sannan hankalinka ya kwanta ko Walid?" Walid ya ɗage kafaɗa ya ce "Duk yadda ka gani" Viper ya hankaɗe shi gefe, ya wuce ɗakinsa, ya rufe ƙofa. Walid ya bishi ya leƙa ta taga ya ce "Me zaka yi ka rufe ƙofa?" Leda ya ciro daga aljihunsa, ya haɗa allura a sirinji, zai yi wa kansa. Walid ya ce "Al'amin, ba zaka daina yi wa kanka allurar nan ba ko? Ba za ta yi maka ba, ka haƙura mana" Al'amin ya tashi, ya je ya ja tagar ya rufe, ya bar walid a waje yana surutu. Sumayya kuwa tun da ta koma gida, mama ta lura da yanayinta, sai dai ta yi zaton ko gajiyar aiki ce, amma har dare ba ta walwala. Dan haka ta magantu, ta ce "Ƴar mama, wai ko babu lafiya ne?" Sumayya ta ce "A'a lafiyata ƙalau?". "To faɗa ku ka yi da mutuniyar ne?" "A'a bamu yi faɗa ba mama" Ba ta gaza ba ta sake cewa "To ko wurin aikin ne suka yi miki wani abun?" Sumayya ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Hajiya mama, bamu yi faɗa da ƴar ki ba, lafiyata kuma ƙalau, kawai kin san yanayin aikin namu ne, kayi ta ganin abubuwa na ban tausayi daban-daban". Mama ta ce "Ai baku ba sumayya, mu ma masu saurare, kusan kullum cikin zullumin kunna radiyon muke, sai dai ku ƴan jarida ku ne idonmu, ta bakinku kawai muke jin wasu labaran da jin halin da duniya ke ciki. Allah dai ya saka muku da alkhairi ya tsare mana ku baki ɗaya, daga ke har Nabilan aikin tainakon al'umma ku ke yi, Ubangiji Allah ya tsare ku ya kawo mazajen aure na gari" Sumayya kamar ta gaya wa mama, abun da aka umarceta a wurin aiki, amma ta san hankalinta tashi zai yi, zata iya hanata aikin ma, kuma Allah ne gatansu aikin nan ne gatansu, dan haka ta ja bakinta tayi shiru. *** Sannu a hankali barrister Naja'atu take bin titin ƙauyen, sai tsaki take yi saboda yadda garin yake babu kyakkyawar hanyar shiga. Sai uwar ƙura da kwazazzabai a hanyar. A hankali ta cigaba da tuƙin har ta ƙarasa in da take son zuwa. Sai da ta shiga tsakiyar tsakar gidan, sannan ta yi sallama. Daga cikin ɗaki a ka amsa sallamar. Daga baya matar ta fito daga ɗakin, ta ce "Waye?" Ganin barrister Naja'atu ya sanya ta ɗan saki fuska, ta bata damar shiga ɗakin. Shame-shame taga rammaa a kwance a kan katifa, ta nemi wuri ta zauna a gefe. Ta kalli in da ramma take, sannan ta mayar da idonta kan maman ta ce "Na dawo ne na ji me kuka tsayar, kuma na ga haryanzu ba ta da lafiya, anya ramma ba shagwaɓa a wannan lamarin? ya ci ace kin ware ai, da auren ma aka yi miki ai da kina gidan miji, ko shi ma hakan zaki yi ta yi masa". Fashewa da kuka ramma tayi, cikin tsananin baƙin ciki da takaici. "Meye kuma na kuka? Wannan abun da ki ke yi, sai mutane sun san halin da ki ke ciki?" Cikin sanyin jiki da damuwa, maman ramma ta ce "Tun da abun nan ya faru, take rashin lafiya, jiya mun je asibitin sha ka tafi, na garin nan, an ce ciki ne da ita" tayi maganar tana fashewa kuka mai taɓa zuciya. Sak Naja'atu tayi, tana kallon su. Ta numfasa ta ce "Wai wannan kukan na menene ku ke yi haka, kukan zai yi muku magani ne? Ai wannan ba abun ɗaga hankali bane ba" Cikin tsananin mamaki, maman rahama take kallon barrister Naja'atu. "Baiwar Allah, ce miki na yi fa, an ce mini ciki ne da ita, wanda ya dubatan ɗan garin nan ne, na san dole maganar nan ta fita, auren yarinyar nan ba zai yiwu ba, amma kina nuna bakomai bane ba, dan girman Allah a karɓowa yarinyar nan hakkinta". Naja'atu ta ce "Baiwar Allah, ko fa an kai yaron nan kotu yayi prison, abun da zai faru ya riga faru, ba kuma zai goge ba, ɓacin suna kuma ya riga ya ɓaci. Matsalar mutanen mu na Arewa, kuna giramama al'ada da addini a kan ƴancinku. Da in da aka cigaba ne, zata iya haife abun da ke cikinta, idan tana so, and rise him as a single mother, har ta iya neman ya din ga biyanta wani abu a kotu, shikenan. But for now, za a iya zubar da cikin ta cigaba da harkokinta sai me? Is an adolescent crises kowa ma zai iya faruwa da shi". Cikin mamaki maman ramma ta ce "Baiwar Allah kuma ke musulma ce?" "Ƙwarai kuwa, muslma ce ni gaba da baya, mafita nake baku da shawara. Zan je na yi booking a saka rana a can cikin gari, private hospital, a cire cikin lafiya ƙalau za a cire shi, yanzu an cigaba nesa ba kusa ba, ku karɓi kuɗin ku ku rage zafi". Rma ta fashe da kuka ta ce "Ni mama tsoro nake ji, an ce mutuwa ake yi, dan Allah ni dai a kai shi wurin alƙali, an ce kina taimako dan Allah ki taimaka mini, ji nake kamar na mutu na huta, ba a taɓa cikin shege a garin nan ba sai a kaina, dan Allah ki taimaki rayuwata, wallahi wanda zan aura ya ji labari ba zai aure ni ba, babu kuma wanda zai ce zai aure ni, cewa za ayi na zama ƴar iska" ta ƙarasa maganar kamar ta shiɗe. Barrister Naja'atu ta ce "And so what dan an fasa aurenki? Zaki iya zama duk abun da ki ke so a rayuwa ko da aure ko babu, waye ya ce muku aure shi ne limit na rayuwar ƴa mace ne? dan Allah ku fuskanci rayuwarku, ku daina bari ana cutar ku da addini da al'ada". Cikin baƙin ciki maman ramma ta ce "Kin ga ya isa baiwar Allah, idan bawa bai riƙe addini ba haka zai ta rayuwa kamar dabba a gari, babu ƙa'ida babu hukunci? Wannan ai salon bawa yaro damar ya je yayi zina ne, ko ni da nake jahila a cikin ƙauyen nan, sam maganarki ba ta da tushe balle makama a wurina, dan haka ki tashi ki tafi kawai, bana buƙatar taimakon naki, cuta ce an cuce mu Allah ya isa kawai" Naja'atu tayi wani irin murmushi ta ce "Ƙarshen abun fa kenan, ki yi Allah ya isa, na biyo miki da masalaha amma kin ƙi, shikenan idan kin ƙi ji ai ba kya ƙi gani ba, duk abun da ya biyo baya wannan shi ne abun da ki ka zaɓa. Sai dai ina sake yi miki gargaɗi da babbar murya, kar ki kuskura ki sake shiga kafafen watsa labarai ki yi magana, idan kuma ki ka sake, ba ruwana" Ta tashi ta sake ajiye musu kuɗi, da complementary card ɗin ta, ta ce "Akwai lambar wayata a jiki, na san zai iya yi muku amfani, idan ku ka ga babu sarki sai Allah, domin kuwa barin cikin nan, dai-dai yake da zama da ajalinta, dan kome zai ɗauka, uban wanda ya aikata laifin, ba zai bari ba" Gaba ɗaya bin ta suka yi da kallo, har ta tashi ta fita, ramma ta fashe da wani irin kuka, tare da jin ƙarshen rayuwarta ya zo. Mahaifiyarta ta kalleta ta ce "Ki yi haƙuri ramma, ina tare da ke in sha Allah, na san ko menene ya faru, ni ce sila, da ban tura ki aikatau ba, da haka ba ta faru ba, amma babu yadda zan yi ne, ki yafe mini dan Allah" tayi maganar tana kuka ita ma. Sumayya na ta aiki a kan computer, sai dai hankalinta baya kan aikin sam, kawai dai tana yi ne, amma ƙasan zuciyarta tsoro da fargabar dalilin da ya sanya, aka ce ta je gidan honorable Indabo ta yi hira da shi take ji, idan a kan laifin da ta yi wancan karon ne, ai ta bayar da haƙuri, kuma lokacin tana farkon zuwa ne. Sallamar murtala ce, ta dawo da ita hayyacinta, tayi murmushin yaƙe ta ce "Uncle murtala, saukar yaushe?" Ya nemi wuri ya zauna ya ce "Agogo sarkin aiki, yakamata a ƙara miki matsayi a gidan nan fa" Ta waro ido ta ce "Ni a wa?" "Ke a ma'aikaciya jajirtacciya mana, wai ya aka yi mutuniyar take ɗaga miki ƙafa yanzu, lawisa?" Sumayya ta ce "Hmm, Arfa ce ta ce na daina jin tsoronta, nima na nuna mata bani da kirki idan ta takura mini, shi ne fa ta sarara mini". "Ai matar nan ƴar bala'i ce lamba ɗaya" Sumayya ta sake tattara nutsuwar sa a kan sa ta ce "Yauwwa ncle murtala, akwai matar da ka yi recording, ta zo an yi raping ƴar ta, an ce Barrister Naja'atu ta shiga case ɗin, ina aka tsaya ne?" Da sauri ya ce "Rufa mini asiri, ni da aka kusa korata a kan case ɗin, kuma lawyoyi da masu kare hakkin ɗan adam, sun yi casa a kan case ɗin, sai dai tun da ta shiga cikin lamarin, kowa ya ja da baya" Sumayya ta ce "Ikon Allah, to ai haryanzu ban ji a ina aka tsaya ba, wai ɗan waye ne yayi?" "Taɓ ba zaki ji mutuwar sarki a bakina ba, nima ba ta faɗa mini ba matar, wai dai yaron ɗan masu kuɗi ne, wai ɗa ne ga wani ɗan majalisa, ba ta san sunansa ba, a gidan ƙanwar ɗan majalisar yarinyar take aiki, sun je gidan ta bi ba'asi, an hana su shiga, masu gadin da suka kai yarinyar asibiti ma duk an canza su" Cikin tausayawa Sumayya take girgiza kai ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, shikenan akwai Allah, amma kana ganin ita Bunkuren za ta yi wani abun kirki a kai? Meyasa ba za a bibiyeta ba, a ji a ina aka tsaya a case ɗin ba, atleast a gurfanar da shi a kotu mana" Ya miƙe tsaye ya ce "Lallai ƙanwata baki san ƙasar nan ba, ai dokar ƙasar nan a kan talaka kawai take aiki, ko ɗan kansila ne, ba za su hukunta shi ba, ita kanta barrister nan akwai ayar tambaya a kan ta, duk da a zahiri ta Allah ce, amma yadda ake tsoronta komai tayi, babu wani mai challenging ɗin ta, akwai wata a ƙasa". "Gaskiya dai, Allah ya sa mu dace " Ya amsa mata da Amin. Nasir yana ta yi wa Nabila bayanin, irin cigaban da yake samu a neman viper, amma hankalinta ba ya kansa, jin sa kawai take yi, kawai ji take kamar ta gaya masa halin da ake ciki, amma ta fasa, dan ta san faɗa zai yi mata. Hankalinta bai dawo jikinta ba, sai da ta ji ya ce zai je Abuja. Ta kalle shi ta ce "Abuja kuma? Me zaka yi?" "Harkar aiki mana, a ƙalla sati zuwa wasu kwanaki" Ta kwaɓe fuska ta ce "Har sati?" "Eh mana, ko in tafi da ke ne?" Tayi murmushi ta ce "Wace ni, Allah ya bada sa'a" Kafin ya amsa, wayarsa ce ta fara ringing, ya ɗaga ya saka a kunnensa, "To" kawai ya ce, ya ajiye wayar ya miƙe ya ce "Bari na shiga sashen mama, tana nemana" Nabila ta ce "To" Agogon hannunta take kallo, yau ko Abba zai jajjagata idan ya dawo bata nan sai ta fita, dan tuni ta ɓoye takalminta da hijjabinta a harabar gidan, za ta lallaɓa ta fice, yadda take ji a ranta, ko zata rasa rayuwarta, ba ta da wani burin da ya wuce ta ga an kama Aminu Viper, domin kuwa shi ne ƙashin bayan matsalar aikin daba da dillancin miyagun ƙwayoyi, gefe guda kuma ga dakon burin da take yi. "Nasiru sau nawa nake gargaɗinka a kan yarinyar nan? Ban isa in gaya maka magana ka ji ba ko?" Cikin son kare kai ya ce "Wallahi mama ba abun da ki ke tunani bane ba, magana muke yi kawai a kan harkar aiki" "Ni ka yi maganar harkar aikin da ni mana. Wai ma yaya muka yi da kai, ina alƙawarin mu?" "Mama dan Allah ki ƙara mini lokaci, sonake na kammala aikin nan na nutsu, kin san komai lokaci ne" A hasale ta ce "Zan kwaɗe ka da kai da lokacin, shekarunka nawa yanzu a duniya, me ka ke nema da Allah bai baka ba? Wato in saki jiki ka ce wannan shegiyar yarinyar zaka aura ko? To wallahi baka isa ba, idan ba ka kiyayeni ba, sai dai ka dawo ka tarar na aura maka duk wadda nake so" Yayi shiru ya sunkuyar da kai, shi bai ga aibun Arfa ba, kuma a zuciyarsa ji yake kamar zai samu chance ɗin da zata zama mallakinsa, rashin gaya mata abun da yake ji game da ita kawai, ba ƙaramin azabtuwa yake yi ba. Sanye take da face mask, tana rarraba idonta, ta ga ta ina zata ganshi. Liti ya kalli Walid ya ce "Ka ganta ko?" "Eh, amma bana ganinta sosai, ta rufe fuskarta da facemask". Liti ya ce "Bari na yi wa gali magana" Nabila na tsaye tana rarraba ido, wani matashi ya zo gabanta ya tsaya, ta ɗaga kai tana kallonsa. "Ki sauke takunkumin fuskarki". Cikin tsiwa ta ce "Ban gane ba, ina ruwanka da ni?" Wayar hannunsa ya ɗaga mata, da take a kan kira, muryar liti ta ji. "Ki sauke takunkumin fuskarki, ko kuma na fasa haɗaku" Waiwayawa take yi, ta ga ta ina za ta ga liti, ta kalli matashin ta ce "Da kai zai haɗani?" Ya girgiza mata kai. Ta din ga waige-waige ko zata ga daga ina liti yake ganinta, har ya san ta saka facemask. Kafin ta waiwayo, gali ya bar wurin. Ta sauke facemask ɗin, tana rarraba ido. Zabura Walid ya yi ya ce "Kai, a ina ka samo wannan yarinyar?" "Jiya ta zo ta same ni, wai ita ƴar uwar viper ce, in taimaka in haɗa su, na shiga area jiya na ɗan yi wuru-wuru, an tabattar mini ita aka kwatantawa dabar madaki, ta je nemansa, suka sakar mata karnuka, ban san waye ya kwatanta mata ni ba". Walid ya ce "Tabbas! Yakamata a haɗa su" Liti ya ce "Idan kuma haɗin baki ne, ko wata maƙarƙashiya ce aka shirya masa fa?" Walid ya ce "Zan kula da komai, amma yakamata su haɗu, ka ce ta dawo jibi da safe" "Kana ganin babu matsala?" "Babu matsala" Nabila ta fara gajiya da tsayuwa, matashin ɗazu ya sake dawowa, ya miƙa mata wayar. Ta karɓa ta yi sallama. "Ki dawo jibi, ƙarfe sha ɗaya za'a haɗaki da shi". Kamar Nabila ta yi zagi, dan haushi, amma ta danne ta ce "To shikenan, Allah ya kaimu" haka ta bar wurin jikinta a sanyaye, har ta fara tunanin ko dai raina mata hankali kawai zai yi. Haka ta koma gida, ba tare da ta ji za ta sare ba. Sumayya daga aiki gidansu Nabila ta je, dan su tattauna a kan umarnin da ta samu a wurin aiki. A ɗaki ta tarar da Nabila, tana bacci, dan daga wurin su liti da ta dawo, kwanciya ta yi. Tashinta tayi, Nabila ta tashi tana tsaki, saboda yadda ta tsani a tashe ta tana bacci. "Ke baccin uban me ki ke yi, bayan azahar, har kin dawo daga aikin ne?" Nabila ta yi miƙa ta ce "Ni ban je aikin ba ma" "Allah ya shirya ki, tashi ki wanko fuskar ki, mu yi magana akwai case Arfa". Nabila ta sake mayar da kanta kan fulo ta ce "Faɗi in ji" "Dalla ki tashi ki saurare ni" "Wai ba kunne ne yake ji ba?" Sumayya ta ce "Kin gane mutumin da muka gani a reception, ki ka ce kin tsane shi? Ɗan majalisa ne" "Yanzu takanas ki ka zo gaya mini ɗan majalissa ne? Ai na sanix Sumayya ta ce "Dalla ki tsaya ki saurare ni, Honorable Ma'aruf indabo ne ai" Nabila ta tashi zaune ta ce "And so?" "Shi ne wai ni zan yi hira da shi, a madadin murtala, amma ya yi waya, wai sai dai na je gidansa na yi recoding ɗin program ɗin, shi ba zai samu zuwa ba" Nabila ta waro ido ta ce "Saboda me?" "Wai ba shi da lokaci, Nabila tsoro nake ji, ko zaki raka ni? Jibi in Allah ya kaimu ne zan je,ba na son rasa aikina, kuma ina tsoron ya cutar da ni" Nabila ta ce "Kash, gashi kuma nima zan je wani aikin ne, da na raka ki aminiya. amma menene a ciki, ke zuwa gidan ɗan majalisa ba cigabanki bane?" A raunane Sumayya ta ce "Tsoro nake ji Arfa" "Sumayya, wani abun fa dole sai mun cire tsoro, tsoronki yayi yawa, ki yi addu'a, duk abun da ya same ki, gidan radiyon will be responsible, babu wani abu in sha Allah, ai mun riƙe addu'a" Yanayin fuskar sumayyan ya tabattar mata da gaske tsoron take ji. Sai dai ita ba ta ga abun tsron kamar yadda sumayya ta ɗaga hankalinta ba. Nan ta din ga jan ta da hira, har ta saki jikinta suka cigaba da hira, suka ci abinci tare. Sai daf da magariba ta raka Sumayya ta tafi gida. Duk da ƙirjin Arfa na tsananta bugawa, amma ba ta ji zata iya fasa abun da ta ƙudurta ba, domin kuwa sai ta ga ƙwal uwar daka, jibin nan za ta shirya ta sake komawa wurin liti. Paid book ne ₦500 via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank Sai shaidar biya ta 08081012143 Special 1k, wanda za su jira complete document shi ma 1k ne. Ayshercool 08081012143 [7/26, 1:37 PM] null: *ƘARFE A WUTA* Arewabooks : ayshercool7724 Watpad: ayshercool7724 What's app :08081012143 What's app channel https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g Paid book ne ₦500 via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda ba ss som group akwai special 1k. 12 Yau ma ba ta sake zani ba, a yanayin da Walid ya iske Viper, ya sha duk abun da yake tunanin zai sha, ya bugu yayi bacci, amma jikinsa ya mutu murus, ya kasa baccin. Idanunsa sun yi jawur, tamkar ana iza wuta, jijiyoyin kansa sun kumbura, sai buɗe idonsa yake yi yana lumshewa. Walid ya kalli ɗan mama ya ce "Ɗan mama kai ka ke kawo masa kayan nan ko?" "Wallahi bani bane ba, da kansa ya fita ya samo abun sa, ban kawo masa komai ba". Ya mayar da idonsa kan Viper ya ce "Ka na ji na?" Ya ɗaga kai ya kalli Walid alamar eh. "Wai ba zaka daina fita ba, sai wani abu ya faru tukuna, ka sake sakamu a matsala?" Viper ya kalli walid, amma yayi masa shiru. Shikenan, ina son zamu fita da kai, zan nuna maka wani abu mai ban mamaki" Viper ya ce "Walid" ya kira sunansa da dakakkiyar muryarsa. Ya amsa da boss "Boss" "Meyasa ba ka da zuciya ne?" Yayi maganar cikin maye. "Na ce bana son sake ganinka" Walid ya ce "Saboda duk sheɗancina, ɗan halak ne ni. Ya zaka bi ni mu je?" "Ba zani ba" "Yakamata ka fara sanin dalilin da ya sa yarinyar nan ta matsa a kan lallai sai ta haɗu da kai, ina..... Cikin hargowa ya ce "Wai wace irin yarinya ce? Meye haɗina da ita? Wacece ita me take nema a wurina?" yadda ya firgice sai da Walid ya matsa baya da sauri. Ya cigaba da cewa "Kowacece, a kawar da ita, bani da alaƙa ta kusa ko ta nesa da kowace mace, kar ka kuskura kar kuma ka fara, idan ba haka ba duk abun da ya biyo baya kai ne sila" Walid ya ce "Na ji na fahimta, easy ka yi haƙuri". Ya ja tsaki, ya yinƙura dan ya tashi da niyyar ya fita, amma jiri ya ɗebe shi yayi baya, cikin zafin nama walid ya riƙe shi, ɗan mama ya taimaka masa, suka kwantar da shi. Ɗan mama ya ce "Da gaske ka ke wai sai ka haɗa shi da yarinyar? Kuma akwai alaƙar tsakaninsa da ita?". Walida ya ce "Shi nake son tabattarwa". "To ya ce baya so, amma kai ba ka tunanin ko ƙarya take yi?" Walid ya ce "Ƙaryar ma take yi, amma yakamata su haɗu" Ɗan mama ya sake cewa "Sai ka haɗa sun kenan, idan ya illata ta fa?" Walid ya ɗora yatsansa a kan leɓensa alamar yayi shiru, dan ya san Viper idonsa biyu kuma yana jin sa. *** A office ɗin su Nasir kuwa, hira ta yi hira, ake gaya wa Nasir, wani ɗan majalisa ne, yayi belin yaran madaki da aka kama, ya saka aka sake su. Cikin takaici ya ce "Allah wadaran naka ya lalace, muna tufka suna warwarewa, mun zama tamkar bayinsu, kullum cikin ganin gazawarmu ake, alhalin muna iya ƙoƙarinmu" Suka cigaba da tattaunawa, a kan yadda manyansu kan yi musu karan tsaye, a kan harkar aiki, da hana ruwa gudu. Ramma ce take ta murƙususun ciwon ciki, hankalin mahaifiyar ta a tashe, take ta ba ta jiƙe-jiƙen magunguna, da ta zuƙa kaɗan sai amai, ba ta iya cin abinci ga wani irin zazzafan zazzaɓi da yake damunta. Kullum ta na ɗaki, ko tsakar gida idan ba dole ba, bata fita, saboda yadda labarin cikin nan ya watsu ya cika garin su, dama ta san isa sai ya bayar da labari, tun da ɗan cikin garinsu ne, ku ma shi ne ya tabattar da akwai cikin. Cikin matsananciyar damuwa ta dubi ramma ta ce "Sannu ramma, na baiwa sani kuɗi ya sayo miki maganin zazzaɓi, kin ga haryanzu babu shi shiru bai dawo ba". Cikin kuka ta ce "Mama mutuwa zan yi". "Ki yi haƙuri ramma, ba zaki mutu ba, kina karya mini gwiwa, ki daure. Amma anya ba zamu yadda a cire cikin nan ba? saboda rufin asirinmu, kuma kema ki huta" Cikin sauri ta girgiza kai ta ce "Mama tsoro nake ji" Rasa abun yi ya sanya maman ramma, sakata a gaba suka cigaba da kuka tare, a zuciyarta ta din ga ja wa Abdul duk wani nau'i na masifa da jafa'i. Yau sumayya za ta je program gidan honorable Indabo, maimakon ta kasance cikin farin ciki, a dalilin zata shiga gidan babban mutum kamar sa, amma ta gaza nutsuwa da yin farinciki a kan hakan, sai wata irin fargaba da faɗuwar gaba da take fama da ita. Sai da ta fara shiga wurin aiki, ta gabatar da ayyukanta na ranar, sannan ta fara harhaɗa kayan aikin da za ta yi amfani da su. Gaba ɗaya jikinta babu ƙwari, sai tsananin tsoro da fargaba. Murtala ne yake ta kwantar mata da hankali, tare da nuna mata, hakan ma wani cigaba ne, ta sani ko daga program ɗin su daidaita da honorable ɗin. Jin sa kawai take yi, tare da murmushin yaƙe. Har bakin motar gidan radiyon da za a kai ta a ciki, yana ƙarfafa mata gwiwa, "Sumayya, abun da zan gaya miki shi ne, ki san iyakar ki a kan program ɗin nan, iya tambayoyin da aka rubuta miki, ki yi masa su zaki yi masa, kar ki ƙetare su ki jawo wa kanki matsala, ƴan siyasar nan ba kowa ne mai imani a cikin su ba" "In sha Allah uncle murtala zan kiyaye, na gode sosai" Ta shiga motar ta zauna, direban ya ja suka tafi. Nabila kuwa tana office tare da barrister Habib, dan yanzu ya saukko ya fara yaba mata, tana ƙoƙari, ya fuskanci kawai shiririta ce take damunta a kan aikin, da rashin mayar da hankali. Tana yi tana kallon agogo, kar ta saɓa lokacin da a ka bata. "Barrister" ta kira shi, ya ɗago yana sauraren ta. "Ban sani ba ko kana jin radiyo" Ya ce "Ina ji mana, meyafaru?" "Cases da dama, idan suka faru mussaman na masu ƙaramin ƙarfi, sai in ga barrister bunkure ta tsayawa mutane, wai ita ba dan kuɗi take aikin ba, dan barrister ce da ba kowa yake iya ɗauka ba, amma tana tsayawa marasa ƙarfi, ko kuɗi ne suka yi mata yawa?" Barrister Habib ya girgiza kai ya ce "Ke dai kawai ayi sha'ani" "Ka san wani abu kuwa? Akwai wani case da wata mata, ta je gidan radiyon su sumayya, ta kai koken an yi wa ƴar ta fyaɗe, an dawo mata da ita daga gidan aiki, ta je gidan da yarinyar take aiki, an hana su shiga, ta kai wurin ƴan sanda, amma ana ta yi mata yawo da hankali, wai yaron ɗan manya ne. To na ji an ce ta shiga case ɗin, amma haryanzu babu wani update, ka san da na so na jarraba sa'a ta, nima na shiga case ɗin ayi da ni, na tausayawa matar da yarinyar, amma na san ana babbakar giwa, wa zai ji ƙaurin zomo, na san ba za ta saurare ni ba ma". Barrister Habib ya tattara hankalinsa a kan Nabila ya ce "Nabila" "Na'am" "Just be yourself, ke dai ki kalli mutum a riga kawai, Naja'atu kura ce da fatar akuya, ba wata abar burgewa ba ce, da zaka yi koyi da ita ba. Yarinyar ƴan siyasa ce, babu wani taimakawa masu ƙaramin ƙarfi, ta fake da wannan ne, dan sunanta ya ƙara fitowa, kuma ya rinjayi ɓarnar da take aikatawa, ai mun yi karatu da ita tare, ƙwalluwar shegiya ce, ke abun bai baki mamaki ba, ace kowace shari'a idan ta tsaya maka, zaka yi nasara, ace komai kai ka ke nasara akwai ayar tambaya ai, dan haka ki yi ta kanki kawai. Duk da mu ma ɗin wasu lokutan, muna take gaskiya, amma yanayin aiki ne ya zo da haka, kuma nata ya ƙazanta". Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Biri yayi kama da mutum" Nabila a zuciyarta ta ce "Idan haka ne, ba gaba da gaba yakamata na yi da ke ba, tona miki asiri zan yi" Habib ya ce "Ya dai?" "Nothing sir, jikina ne yayi sanyi kawai na gode sosai da bayaninka" Ba tare da neman iznin kowa ba, ta ɗauki jakarta ta fita. A in da ta tsaya shekaranjiya, nan ta je ta sake tsayawa, tana fatan Allah ya sa ba jirgata za su yi ba. Ta shafe a ƙalla awa guda a wurin, har ta sare zata tafi, matashin da ya kai mata waya, liti yayi mata magana da ita, ta gani a gabanta. Bai ce mata uffan ba, ya miƙa mata wata takarda. Sunan wata unguwa ne a jiki,da dai-dai wurin da zata je ta tsaya, saboda tsabar wauta da rashin hankali, ta yi masa godiya ta tari abun hawa ta nuna masa takardar. Mai baburin ya gaya mata kuɗinsa, babu neman ragi, ta afka ciki ta ce su tafi. Lissafin da take ma a zuciyarta, na mamakin yadda Naja'atu tayi mata kallon ƙasƙanci ne, ta wulaƙanta ta alhalin ma ba wata mutuniyar arziki ba ce. Babban abun da ta fuskanta, ƙasar nan ba zaka taɓa samun wasu damarmaki ba, har sai ka taka wani babban matsayi na musamman, ka shahara sai dai hanyoyin bi a shahara ɗin ne, ko da kasada ko ka kauce hanya. Ta yi wa kanta alƙawarin, dole za ta bibiyi case ɗin yarinyar nan, ba naja'atu ba, ko a hannun ƙaramar hukumar bunkuren case ɗin yake, sai ta bibiya, ai da ƙananan kasada ake babba, ga kuma babban target ɗin ta, Viper, ta san idan aka kama shi, dole a sara mata, ta shiga cikin mata da suka kafa tarihi. Da wannan gurguntaccen tunani na Nabila, mai cike da wauta da rashin lissafi, suka cigaba da tafiya can ta ce "Malam, wai haryanzu ba a zo ba?" "Ba ki taɓa zuwa unguwar ba ne?" Ta ce "Eh, sai yau zan fara" Ya ce "saura kaɗan in sha Allah" Sai dai gabanta ya fara faɗuwa, tun bayan da ta ga sun bar cikin mutane, sun fita wajen gari. Dai-dai wani gidan gona ya ajiyeta, wurin duk shuke-shuke, da alama akwai mutane a daf da wurin, amma sai an yi tafiya kan a tarar da in da suke. Shi kansa titin wurin, babu ababen hawa da suke kaiwa suna komowa a wurin. Sai rukunin manya manyan kamfanunnuka a wurin, na shinkafa da na taki, wurin shiru sai ƙarar injinan da masana'antun ke amfani da su. Sai da ta sallami mai a daidaita sahun, sannan ta fara tunanin, to ina ma za ta nufa? Tsayawa ta yi, tana waige-waige, kawai ta hango wani mutum ya tunkarota, nan ta fara ja da baya, tana tunanin ko zurawa za ta yi da gudu. "Mu je" ya ce mata a kausashe. Ta turje ta ce "Ina?" "Ba ke ce baƙuwar Viper ba, mu je" A raunane cike da tsoro ta ce "A'a, ka kirawo shi mu yi magana a nan, ni dama kaya nake son saya a wurinsa" Cikin mamaki ya kalleta ya ce "Wani irin kaya?" "Wanda yake sayarwa" tayi maganar a tsorace tana kallon Walid. Ya gyaɗa kai ya ce "Baki san waye shi ba amma? Kin yi kasada nafi muni, wuce muje kafin na saraki biyu a wurin nan" Cikin rawar jiki ta ce "Dan Allah ka yi mini rai, ni ka kirawo shi nan kawai". "Wallahi zan saɓa ki a ka, wuce mu je" Salati Nabila ta din ga yi, dan tun da ta yo dakon kasadar nan, sai yanzu ta ga zunzurutun wautar da ta aikata. Ya sakata a gaba, suka nausa bayan kamfanunukan. A can gidan honorable kuwa, yana da office a cikin gidan sa, in da yake ganawa da mutane na mussaman. Hankalin sumayya ya ɗan kwanta, bayan da ta ga mutane na shiga suna fita a gidan, da alama ba shikaɗai ne a gidan ba, kuma gidansa ne da yake zaune da iyalinsa. A harabar gidan aka dakatar da wanda suka rako sumayya, aka ce itakaɗai za ta shiga. Wani security yayi mata jagora, zuwa wani sashe na gidan, ya kaita wani falo, ya ce ta jira a nan, ta samu wuri ta zauna, a kan kujera, tana zaune a falon office ɗin, tana ɗan kalle-kalle, tana jira kamar yadda aka umarceta. Cikin office ɗin kuma, Barrister Naja'atu ce suke magana da honorable. "Ni fa na yi iya ƙoƙarina, amma da alama mutanen nan, su na da taurin kai, juyin duniya sun ƙi saduda, sai iƙrarin a karɓar musu hakkinsu suke yi, ina ga kawai a ɗauki matakin da ya dace a kan ta". Indabo ya ce "Lallai dama haryanzu akwai masu ƙi faɗi a talakawa?" "Akwai su fa, ku kuna gefe, mune muke shiga cikinsu da rufe bakunanansu a kan ɓarnar da ku ke aikatawa, sai dai kan mage ya fara wayewa, babban abun damuwar sun gaya mini an tabattar musu tana da ciki" Yayi saurin ɗaga kai ya kalleta "Ciki kuma? Sau nawa yayi mata fyaɗen ne?" Ta ɗage kafaɗa ta ce "Wannan kuma shi za ka tambaya, ba zan iya cigaba da ɓata lokacina a kan wannan kucakan mutanen ba, ina da abubuwa masu muhimmanci kawai ayi abun da ya dace". Yayi ajiyar zuciya ya ce "Abdul, ban san lokacin da zai yi hankali ba, ina tsoron lokacin zaɓe, a samu wani ya fito da miyagun halayensa, in the next couple of years, sonake ya samu ref, ko deputy governor a tsayar da shi takara, saboda yarjejeniyar da muka yi, da jam'iyya kenan kafin na yarda na zauna a cikinta, amma al'amarin sa kullum ƙara lalacewa yake yi" Barrister Naja'atu ta ce "To, gara dai ka san abun yi" "Anyway, shikenan, ki tura mini address ɗin su ita yarinyar, za ayi abun da aka saba" ta miƙe tsaye ta ce "No problem" Ta buɗe ƙofar office ɗin ta fito, kallo ɗaya sumayya ta yi mata, ta gane ta, saboda yadda Nabila take ɗora hotonta a status ɗin ta a baya. Cikin son tabattar da abun da Nabila ta gaya mata, a kanta, ya sanya  ta tashi da sauri tana murmushi ta ce "Barrister Naja'atu Bunkure, baya goya marayu, dama zan ganki ido da ido?" Sumayya ta yi maganar tana murmushi. Kamar ta ga kashi, ta yatsuna fuska ta ce "Sannu". Sumayya ta maze ta ce "Na tsinci dami a kala yau, ni ƴar jarida ce, a cikin ayyukan da ki ke gudanarwa, zan so yi miki tambaya ɗaya zuwa biyu, na san masu sauraronmu, za su ji daɗin hakan, kasancewar ki abar so da koyi ga al'ummar mu, mussaman mata. Dan akwai sister na, die hard fan ɗin ki ce, ita ma lawyer ce. Cikin fusata Naja'atu ta ce "Ke saurara mana, daga ganina sai tsare ni ki hau zuba dan kina ƴar jarida, who permits you to do that?" Sumayya ta dake ta ce "No, barrister, ba as ƴar jarida ba kawai, as a woman and one of your fans, ko ƙorafi ne da ni, ta yaya zan same ki ki tsaya mini, atleast ko mintuna uku ki bani mana, dan Allah. Na san ƴan jarida wasu lokutan mu na da zaƙewa amma a duba roƙona" kamar ta zagi Sumayya, ta tsani baƙin naci irin na ƴan jarida, amma sanin halin su na yanzu sai su samu abun ɗorarwa ta ɓata mata career ya sanya ta danne ta ce "Ina jin ki" Fitowar honorable, ta sanya ta yin shiru, ya kalli sumayya ya ce "Mu je in da zaki ɗauki program ɗin" Tana ji tana gani, Naja'atu ta tafi. Can wani surƙuƙi ya ja ta, da sai da ta fara jin tsoro, sai dai duk in da suka ratsa, akwai ma'aikata. Sumayya ta sha mamakin, irin dukiyar da aka yi ɓarna, wurin gida wannan gida da kamar ba za a mutu a bar shi ba. Daga ita sai shi a ƙaton falon, mai ɗauke da ɓangarori daban-daban. Yayi mata iznin zama, yana ƙureta da idonsa, ta fito da kayan aikinta, ta fara saitawa, tana ta addu'a a zuciyarta, dan kaɗaicewar nan ta su kawai, hankalinta a tashe yake. Nabila kuwa, Walid sakata yayi a gaba, har suka zo ƙofar wani gida, a can bayan kamfanunukan nan, babu kowa a wurin, ba gida gaba babu a baya, sai ma wani uban dutse idan ka yi tafiya can gaban gidan, ba ta taɓa zaton akwai irin wannan wurin a kano ba. Ya kalleta ya ce ta shiga. Jikinta yana rawa ta ce ba zata shiga ba, sai dai ya kira wo mata shi nan waje, wanda har a lokacin idan ta ganshin, ba ta san me za ta ce masa ba, tsabar fitina ce da son ta ɗaukaka ko ta halin ƙaƙa ya sanya take wautar. Wani makami ya zare mata, mai kama da kibiya ya buga mata tsawa ya ce "Ki shiga na ce" sai a lokacin ta tabattar da ta tafka babban kuskure, haɗi da wauta mara amfani, idan suka illata ni fa?" Ta tambayi kanta cikin tashin hankali, haka ta shiga, yana bin ta da wuƙa. Ɗan mama yana ɗan matsakaicin tsakar gidan, yana wankin kayansu, jin kukan mace ya sanya shi ɗaga ido, cikin tsananin mamaki. Sai dai yayi wata irin zabura ya ja da baya, yana bin su da kallo. Yana cikin ɗaki a tsaye ƙyam, kamar an gina shi, ya bawa ƙofar baya, yana kallon bango. Ya sha ya bugu, amma bai samu yadda yake so ba, tunanin da yake son dainawa ya kasa, dan haka yana tsaye, yana ta nazarin abubuwa daban-daban a cikin ransa. Ɗan mama biyo su yayi, yana bin Nabila da kallo. Turus Nabila ta yi, duk da ba ta ga fuskarsa ba, amma yanayin suffar jikinsa, sai da ta ji tamkar ta zunduma ihu, kallo ɗaya zaka yi masa ka san madakin maza ne, ingarman namiji ne, da Allah ya yi shi da tsawo da kuma kakkauran jiki. Idonta ya sauka a kan miyagun makaman da suke ɗakin, kamar za aje yaƙin duniya, gefen katifar da take ɗakin kuma, sirinjai ne, da kwalaban allura a wurin, sai kuma satchets na magunguna da kwalabe da kwalayen sigari. Ban da warin sigari, da wani irin ƙauri da ba ta gama tantance ko na menene ba, babu abun da yake tashi. Tirƙashi! Ai ko lokacin da aka rufta ta, aka turata dabar madaki, ba ta ga abun da ya razanata ba, kamar yanzu ba, dan tarin ƴan dabar da ta tarar na su wasa ne, ba su firgita ta ba, tun da ta samu ƙwarin gwiwar yi musu magana. "Boss, ga ta na kawo maka ita, sai ka ji dalilin da ya sa take nemanka" Babban abun da ya ƙular da Viper, bai wuce watsi da umarninsa, da Walid yayi ba, tun da fari ya gargaɗe shi, a kan kawo masa wata mace, dan ba shi da alaƙa da su, amma ya yi burus da maganar sa. Kasancewar ya sha sai dai buguwar ta gagara yadda yake so, ya sanya ƙwayoyin suka taimaka wurin tunzura shi, ya waiwayo a fusace domin ya sauke wa Walid rashin mutunci. Sai dai gabansa yayi wata irin mummunar faɗuwa, adadin bugun zuciyar sa ya ƙaru da sauri da sauri, wani irin gumi ya fara tsatstsafowa ta kafafen gashin sa, jijiyoyin jikinsa suka kukkumbura. Shi dai ya san a farke yake, ba iya bacci yake mai nauyin da zai ɗauke shi, har ya sa shi mafarki yake, balle ya ce mafarki ne, kuma ya san a hayyacinsa yake, domin kuwa bai yi buguwar da hankalinsa zai gushe ba. Sai dai a zahiri, sam yanayin sa bai nuna irin halin da ya shiga ba, dan babu abun da ya canza a tattare da shi, ya zuba mata manya-manyan jajayen idanunsa. Tirƙashi! Jin ka ya fi ganinka! Nabila za ta iya cewa, tun da Allah ya sa ta buɗi ido a duniya, ba ta taɓa ganin mutum mai kwarjini da razanarwa kamarsa ba, kodayake ai ya wuce ta kira shi kwarjini, sai dai mai ban tsoro. Yadda ake faɗarsa a baki kawai, ta ɗauka wani ƙaramin alhaki ne kawai, sai dai yanzu ta tabattar da  ya wuce duk yadda ta yi tsammanin ganinsa sa. Ashe waɗanda take gani ƙaryar daba suke yi, ga ɗan daba na gaske yau ta gani,kamar ta fashe da kuka a cikin zuciyarta ta ce "Na shiga uku, wani tsautsayin ne ya kawo ni? Daga ni sai su idan suka kashe ni fa? Na san ko gawata ba za a gani ba, balle ayi mini salla, kamar yadda addini ya tanada" So take ta ɗaga ido ta kalle shi, amma abu ya gagara, saboda daga kallo ɗayan da ta yi masa, ba ta fatan sake yi masa na biyu, duk da zuciyarta na azalzalar ta, ta sake yin hakan, ba zata iya tantance abun da take gani a cikin idanuwanta ba, da kuma ma'anar irin kallon da yake yi mata ba. Ƙoƙarin sake satar kallonsa tayi, amma suka yi ido huɗu, tayi saurin sunkuyar da kanta ƙasa, saboda mummunar faɗuwar gaban da ta ziyarci zuciyarta, tabbas cikakken mashayi ne duba da yadda launin idanunsa suke, sai dai Allah ya yi shi da siffar girma da cikar zati, ya isa a kira shi da cikakken namiji. "Shi kuwa wannan meya haɗa shi da aikin daba, a irin ƙira da Allah ya yi masa, da aikin office ya dace, ko na tsaro, ya ɓata wayonsa, da ya ƙare a shaye-shaye da daba. Duk da ta sunkuyar da kanta, a tsakiyar ƙirjinta take jin kallon da yake yi mata. Walid ya zagaya saitin kunnensa ya ce "Ka ga abun da nake gaya maka?" Jinjina masa kai kawai yayi, taku ɗaya yayi, ba tare da Nabila ta ankara ba ya danƙi wuyanta. Ba wani riƙon kirki yayi mata ba, amma idanuwanta suka yo waje, jikinta ya hau kyarma, tamkar ana kaɗa mata gangi. Ta saka hannunta ta riƙe nasa, numfashinta na fita da sauri da sauri, cike da tsoro take ta gwagwarmayar ƙwatar numfashinta, saboda yadda take jin yana barazanar barin ƙirjinta. Ba ta ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da ta ji tsini a cikinta, ga wani irin azababben zafi da ya ratsa fatar cikinta. Ba ta san bata tsorata ba, sai da ya buɗe baki yayi magana. "Wacece ke? Me ki ke nema a wurina?!!" Numfashinsa ya sauka a fuskarta, warin sigari ya daki hancinta, jikinta ya hau tsuma. A rikice Walid ya ce "Boss zaka kashe ta fa, ka kalli abun da ka ke yi" Bai saurari walid ba, ya sake buga mata tsawa, tare da ƙara nutsa wuƙar da ya saita a cikinta. "Viper, jini ya fara zuba daga cikinta, ka dawo hayyacinka mana" yayi maganar yana ƙoƙarin kai hannu ya ƙwace wuƙar hannunsa. Idan ka taɓa ni, kai zan cakawa!" Yayi maganar yana kallon idon Nabila da suka yo waje, ga jikinta ya saki, sai numfashi da take yi da kyar. Buɗe baki tayi, da niyyar ta yi magana, amma jikinta ya saki, ta daina ganin komai sai duhu. "Viper kar ka kashe yarinyar nan" Amma kan walid ya yi wani yinƙuri, Viper ya watsar da ita a wurin, ta faɗi sumammiya. Ayshercool 08081012143                  *ƘARFE A WUTA* AISHA ADAM AYSHERCOOL Arewabooks : ayshercool7724 Watpad: ayshercool7724 What's app :08081012143 What's app channel https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g Paid book ne ₦500 via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda ba ss som group akwai special 1k. 13 Cike da takaici Walid ya nufeta da sauri, ya kalli Viper ya ce "Amma meyasa zaka yi haka? Da ka kasheta fa?" Aminu ya kalli saman tsinin wuƙarsa da take ɗauke da jinin Nabila, bai kalli Walid ba ya ce "Ban gaya maka kar ka kawo mini kowa ba?" Walid ya ce "Ka gaya mini, amma na tabatta ka ga abun da nake son ka gani, ai ko?" "And so, me hakan zai amafana mini? Ka ƙaddara ban ga komai ba, kuma gargaɗi na yi mata a kaina, dole na san tana da manufar son haɗuwa da ni, wataƙila wata ƙulalliyar ce, sai dai amafani da mace ba zai hana in illata ta ba, idan ta shiga gonata" Walid ya ce "Yanzu abun da ka gani, ba shi da muhimmanci kenan?" "Ko kaɗan" ya bashi amsa kai tsaye. Walid ya tsuguna a kanta, amma ya rasa abun da yakamata yayi. Wani irin numfashi Nabila ta fara fitarwa, mai sauti wanda hakan yake tabattar da, numfashin yana ba ta wahala. Ɗan mama ya ce "Mun shiga uku, wane irin numfashi ne wannan,ko mutuwa za ta yi ne?" Walid ya sake dirircewa ya rasa abun yi. Viper ya goge jinin Nabila da ke jikin wuƙarsa, a jikin rigarsa. Ya ɗaga kai, yana kallon yadda take jujjuya kanta, tana neman iska. Wata drower ya saka mukulli ya buɗe, ya ɗaukko wata ƴar ƙaramar akwati, ya ajiye, ya ƙarasa ya ɗauki jakar Nabila, ya zazzageta yana neman inhaler, amma bai gani ba, ya ja uban tsaki ya tashi, ya sake buɗe wardrobe, ya ɗaukko inhaler, sai dai sai da ya tsaya yayi ta kallon inhaler, yana kallon Nabila, sannan ya ƙarasa kanta, ya tsaya, ya ɗagota ya fesa mata a cikin bakinta. Kamar zata haɗiye inhaler, haka take sake buɗe bakinta, ya mayar da ita ya kwantar, ya ɗaga gefen rigarta, da wuƙarsa ta huda, ya saka auduga da spirit, ya goge jinin tsaf, ba wata huda ce ta kirki ba, kawai dai ta zubar da jini ne sosai. Gaba ɗaya suka zuba masa ido, ya zuba iodine a jikin audugar, ya saka a kan cikin nata, ya kawo plasta, ya saka. Dama ya saba yi musu dressing, idan suka je aka sare su, a wurin rashin jin su. Ya mayar da akwatin in da take, ya koma gefe ya kunna sigari. Mamaki yake da tunanin, uban me take nema a wurinsa, sai dai ya fi yarda da cewa, tarko ce ake son yi masa da ita. "Amma ya aka yi, aka samu wannan coincidence ɗin?" Ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa. Duk suka koma gefe, suka zubawa sarautar Allah ido. Tari ta fara yi, ta yinƙura ta tashi zaune, ta kalli kayan cikin jakarta, da suke a watse, ta fara tattara abun ta, sai kuma ta dawo hayyacinta,bayan da suka yi ido huɗu da shi. A rikice tayi jifa da jakar, ta ƙwala wani uban ihu, nan take mafarkin da ta taɓa yi ya dawo mata, tabbas sai yanzu ta fuskanci inuwarsa take gani a mafarki. Ƙoƙarin tashi take ta gudu, cikin zafin nama, ya bar in da yake ya cafkota. Tausayinta ya kama Walid, tare da dana sanin kawo wa Viper ita, ko haɗa bakin aka yi da ita a cutar da shi, atleast ita macece ya ɗaga mata ƙafa, amma ya san in da ya matsa, sai Viper ya illata ta fiye da yanzu. "Waye ya aiko ki?" Yayi maganar a kausashe. Ta girgiza kai, amma ta kasa magana. "Waye ya turo ki na ce?" Yayi mata tsawa. A rikice ta ce "Wallahi ba kowa" tayi maganar tana zubar da hawayen tsoro. "Me ki ke nema a wurina?" "Dan Allah ka yi mini rai, na tuba na bi Allah, ba zan sake ba, dan Allah kar ka kasheni, wallahi ni marainiya ce, tayi maganar tana kawar da kanta gefe, ta kasa kallonsa, sai azabar bugu da zuciyar ta take yi, cikin tsoro da fargaba. "Look up kalleni" muryarsa ba a iya kunnuwanta take jin ta ba, a tsakiyar zuciyarta take yi mata amsa kuwwa, gashi ya matso daf da ita, warin sigarin da yake yi, ya fara hautsina mata ciki. "Kalleni" ya sake maimaitawa. Ɗan mama ya ce "Ki bi umarninsa, ba ya maimaita magana, kan ki farka a lahira". Cikin karkarwa, ta ɗaga kanta, da gefen idonta kawai ta kalleshi, amma ta fashe da kuka "Wallahi tsoronka nake ji, ba zan iya kallonka ba, idonka tsoro yake bani, dan Allah ka yi haƙuri kar...... Tsit tayi, ta haɗiye wani irin mugun yawu, da ta ji tamkar ta haɗiyi wuta, biyo bayan ganin ya saita  kaifin wuƙa a kwaroron maƙogwaronta. "Idan ki ka bari, na sake ganin fuskarki, ko a kan hanya, Wallahi sai na kashe ki!" Nabila ta gama saddaƙar da gumin da yake bin ƙafafuwanta, fitsari ne ba gumi ba, gashi tun daga goshinta, har cikin jikinta gumi ne kawai yake yanko mata ko ta ina. Ta jinjina masa kai, ya ja da baya, ya kalli Walid ya ce "Ta ƙara mintuna biyar a gabana, sai dai ka fita da gawarta" Walid ya kalleta ya ce "Zo in fitar da ke hanya" "To in ɗauki jakata?" Tayi maganar cikin tsoro. Walid ya ce "Hanzarta ki kwashe kayanki mu tafi" Sai dai ta kasa motsawar, ta ƙame a jikin bangon ɗakin, jikinta sai tsuma yake yi. A fusace Walid ya ce "Ki tattaro mu tafi mana" Nabila ta fashe da kuka, ta ce "Wallahi tsoro nake ji, kar in durƙusa ya kashe ni, dan Allah ka bashi haƙuri, kar mu haɗu a wani wurin ban sani ba ya kasheni, ya rantse sai ya kasheni". Walid ya ce "Na ji zan bashi, taho mu tafi" "Wallahi na kasa motsi" tayi maganar hawaye na cigaba da zuba daga idonta. Gaban wardrobe ya je ya tsaya, ya juya musu baya, ya saka hannayensa, ya kama ƙasan rigarsa zai cire ya canza wata, kamar wadda ya kwance daga ɗauri, dama idanunsa ne igiyoyin da suka ɗaureta, ta durƙusa ta kwashi kayan jakarta, da jakar ta fita da gudu, ta kwashi takalmanta, ta fyalla a guje, ta bar gidan. Dariya ɗan mama ya ƙyaleƙyale da ita, ya yi wata irin ashariya ya buga ƙafa, sannan ya je gaban Viper yayi wata irin kururwa, cikin sara masa tare da kambama shi ya ce  "Maza gumbar dutse, ina gwanin wani ga nawa, gaba salamun baya salamun mutumina, zaki ka ke sarki a gida sarki a dawa, ina mazan suke, ga fa uban ɗakina wanda ake kira namijin gaske. Sun buga da kai sun barka mutumina, Allah ya baka duniya lahirar ma ka samu in sha Allah. Mahadi mai dogon zamani. Kai idan ba namijin gaske ba, kalli yadda ka mayar da mai hankali zararre cikin ƙanƙanin lokaci, kalli yadda yarinyar nan ta firgice ta koma zararriya lokaci ɗaya, ba gaba da gaba ba ko ta baya sai an shirya tararka uban gidana, mahadinmu mai dogon zamani, Allah ya baka tsawon rai, ya kaimu ranar da zamu ba da jininmu domin ɗaukar maka fansa" Geɓare baki Viper yayi kamar zai yi murmushi, dan kirarin ya tuna masa wasu abubuwa da dama da suka shuɗe. Walid kuwa gaba ɗaya daga Viper har ɗan mama haushi suka bashi, kamar ya ɗura musu ashar, Nabila ko da cunen aka yi musu da iya, shi yaƙi ai ɗan zamba ne, kuma ko ba komai mace ce, bai kamata ya razanata har haka ba, tun da ya san mazan ma razana su yake yi. Takalmansa ya saka,  ya bi bayan Nabila, dan yadda ta fita a burkicen nan, komai zai iya faruwa, gashi ga dukkan alamu, ba ta da cikakkiyar lafiyar numfashi. Viper kuwa, rigar jikinsa ya canza, Ɗan mama ya ce "Boss, wai ka taɓa karatun likita ne? Na san dai ka iya wankin ciwo, to kuma na ga yau kayi aikin likita". Al'amin ya girgiza kai ya ce "Ko ɗaya, na zauna da mai irin ciwon ta ne" Ɗan mama ya ce "Na fahimta, amma dai ba fita zaka yi ba ko?" "Zaka hana ni ne?" Da sauri ya ce "A'a wane ni, ka san idan wannan jarababben ya dawo, ya tarar ka fita, masifa zai ta yi mini" bai saurari ɗin mama ba, ya bi ƙofa ya fita. Nabila kuwa tun da ta fita da gudu, ba ta tsaya a ko ina ba, sai da ta fita titi, shi ma babu ababen hawa, haka ta cigaba da tafiya tana waige-waige, sai a lokacin ta ji gefen cikinta, yana ta yi mata zugi, ta ɗaga rigarta ta ga plasta. Ga jikin rigarta da jini, a hankali ta furta "Na shiga uku" Addu'a ta din ga yi, tana cigaba da tafiya, cikin ikon Allah, Allah ya kawo mai a daidaita sahu, ta kama ta shiga, tana ta haki. Sumayya tamkar yau ta shiga harkar aikin jarida, haka tattaunawar ta su da honorable Indabo take kasancewa, saboda yadda ya tsatstsareta da manya-manyan jajayen idanunsa, yana yi mata wani irin kallo, gashi daga shi sai ita a wurin. Ajiyar zuciya ya yi ya ce "Meyake damunki ne? Ki nutsu mana" Ta jinjina masa ta kai, ta cigaba da yi masa tambayoyin da su aka yarje mata ta yi masa. Sai dai ita kanta ta san amsoshin da yake bayarwa, na son zuciyarsa ne kawai, ba wani abu ba. Jin ta yi shiru, ya sanya ya kalleta ya ce "Ya dai?" Cikin girmamawa ta ce "Tambayoyin sun ƙare sir" "Kamar bakinki akwai magana, akwai tambayoyin da ki ke son yi mini ko? Mu je zuwa ina saurarenki" Ƙasan zuciyarta ta ce, ina ma da gaske ka ke, da ka ji ruwan tambayoyin da ko ka ƙi Allah, sai ka dangana da faɗar gaskiya, a zahiri kuwa ta girgiza kai ta ce "Babu sir" Ya kalli kofunan gabansu, ɗauke da shayi, wanda shi yana yi yana shan nasa, ita kuwa ko taɓawa ba ta yi ba. "Ya ba ki sha shayin ba? Ki sha mana" Sumayya ta sake risunar da kai ta ce "A ƙoshe nake ne" Ya ce "I see, amma na yi mamaki da ki ka ce mini baki da tambaya a gare ni, duk da yadda ki ka ƙaryata hirar da na yi kwanaki, ki ka ce ban yi ayyukan da na ce na yi ba, na ƙyale ki ne kawai saboda managernku yayi ta bani haƙuri, kuma ke mace ce yarinya ƙara ƴar cikina. Siyasa mu tamkar business take a wurinmu baby girl, we invest to make a profit, ita kanta gidan radiyon da ki ke aiki da su, nike hannun jari mafi tsoka a cikinta, dan haka abun da nake so shi ake yi, kuma domin yi mini campaign ya sanya na zuba kuɗina a harkar gidan radiyon" Sumayya dai ta yi shiru, ba ta ce komai ba. Ya miƙe tsam, ya zagaya ya zauna a kan kujerar da take kai, wanda hakan ya sanya ja da baya, tana maƙale jikinta. "Mun gama abun da ya kawo ki, sai kuma abun da ya sa na ce a turo mini ke" Da sauri ta ɗaga ido ta kalle shi, tana mamakin abun da ya faɗa. Ya ɗauki kofin shayinta ya sha, sannan ya ce "Yarinyar da na ganku tare, ranar da na yi zuwan ƙarshe, ita nake nema ba ke ba, amma ke ce tsanin da yakamata na taka na kai gare ta, wacece ita?" A tsorace take kallonsa, ya ce "Ki amsa mini mana". "Nabila ce, ƙawata ce, she's like a sister to me" ta faɗa a tsorace. "Ba wannan nake son ji ba" yayi maganar yana sunkuyowa daf da fuskarta. "Wacece ita?" Sumayya ta ce "Ƴar wani tsohon soja ce, dan Allah idan wani laifin tayi maka ka yi haƙuri, ba zata ƙara ba, idan ma dan ba ta gaisheka bane ranar, dan Allah ka yi haƙuri ba zata sake ba, ba ta da lafiya ne ranar" Ya girgiza kai ya ce "Ko ɗaya, tarko nake son na yi da ita, aiki za ta yi mini" Jiki na tsuma Sumayya ta ce "Wane irin aiki kuma?" Ya gyara zamansa ya ce "Kin san wani ɗan daba Aminu Viper?" "A'a ban san shi ba wallahi" Indabo ya ce "Kina ƴar jarida, ki ce mini ba ki san shi ba, jami'an tsaro na neman sa ruwa a jallo, na yi niyyar shafe tarihinsa, aka samu wani ya yi mini zagon ƙasa, ya rusa mini komai. Har a yanzu ana ta ƙoƙarin kama shi, kwatsam na ganku, kuma na ga tana da wani abu da zan iya yi masa tarko da shi ya zo hannuna, dan haka ƙawarki za ta yi mini aiki" Hankali tashe ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri, mutumin da yake kashe mutane, tana mace ina ita ina ɗan daba, ba jami'an tsaro suna nemansa ba? Za su kama shi dan Allah ka ƙyale mu" Yayi wata muguwar dariya ya ce "Kin san waye indabo kuwa? Kama Aminu ya zama gawa ne kaɗai zai samar mini da nutsuwa da kwanciyar hankali, dan haka dole ƙawarki za ta yi mini aiki" Ta buɗe baki za ta yi magana, wayarta ta fara ringing, ta ɗauka ta duba, ta ga nabila ce take kiranta. Ya ƙureta da idonsa ya ce "Ɗaga mana, ɗaga wayarki" Jiki na rawa ta ɗaga, ta kara a kunnenta. "Sumayya kina ina ne?" Muryar Nabila ta fito raɗau a wayar. Sumayya ta ce "Ina nan ƙalau, lafiya kuwa? Na ji kamar kina numfashi da ƙyar, ciwon ne ya tashi" "Sumayya na kusa mutuwa yau" tayi maganar tana sauke numfashi. A rikice sumayya ta ce "Mutuwa kuma, lafiya" "Na haɗu da Viper, ya kusa kashe ni" Ras gaban sumayya ya faɗi, indabo ya ƙura mata ido, yayi mata alama ta cigaba da wayar. Jiki a sanyaye Sumayya ta ce "To maƙaryaciya, ni zaki jirga?" "Wallahi ba ƙarya nake yi ba, ya na ji muryarki kamar wadda aka ritsa, kin je hirar ne? Ko wani abun ya faru ne?" Sumayya ta ce "A'a, maƙaryaciya, mutumin da ake nema ruwa a jallo ki ka gani bai kashe ki ba?" "Ban sani ba, tun da kin ƙaryata ni ki je ki ƙarata, ina fatan dai mutumin nan bai yi miki wani abun ba, dan mutumin nan yayi ruwan ƴan iska" Kallonsa sumayya ta yi, sannan ta ce "Mu haɗu a gida" Nabila ta ce "Ai dole mu haɗu yau, akwai magana, zan biya asibiti numfashin zai ɗauke, ki kula da kanki dan Allah, jikina yana bani kamar akwai matsala a in da ki ke, idan da wani abu, ki sanar da ni" "Ke normal ne, sai mun haɗu" ta kashe wayar tare da kallon honorable Indabo ta ce "Wallahi ƙarya take yi, ba wani Viper da ta haɗu da shi, yayanta ne jami'in tsaron da yake bincikensa, amma wallahi ƙarya take yi" Cikin ko in kula, indabo yayi dariya ya ce  ce "Wato na yi zubin ƴan iska, wato a  rayuwata ni mutum ne mai sa'a, na tsinci dami a kala, yanzu ke zaki yi mini aikin ba ita ba. Dole ki tabattar idan da gaske take ko akasin haka ki sanar mini, duk wani aiki ko bayanai da nake son samu, ke zaki nemo shi a wurinta, idan ki ka saɓa umarnina kuma, zan saka a kawar mini da ke da ita baki ɗaya!" Sumayya gabanta ya faɗi, ta rasa abun yi, kamar ta kurma ihu, wannan wace irin ƙaddara ce, ace babban mutum kamar wannan da ake ji da shi a kujerun iko, na ƙasa da jihar nan, ya rasa wanda zai saka a gaba sai su ƴaƴan cikin sa. Ya ce "Buɗe wayarki ki bani" tamkar shashasha, haka ta cire password ta miƙa masa, yayi ƴan danne danne a jiki. Wani mutum ne yayi sallama, ya shigo, ya ce "Gani sir" "Wannan wayar zaka yi wa aiki" Ya ce "Ok sir" ya karɓi wayar yana daddanawa, sannan ya miƙowa Indabo. Ya ce masa "You can leave" Ya miƙa wa Sumayya wayar ya ce "Daga yanzu za ki din ga karɓar umarnin, abun da ake buƙatar ki yi, idan ki ka saɓa umarnin, zaki yi dana sani mara amfani, dan sai na fara da wulaƙanta rayuwarki, na tozarta ki, kodayeke dama wulaƙantacciyar ce. Dan ku ƴaƴan talakawa baku da wani amfani, kuma babu wani abu da zai faru idan na salwantar da rayuwarki, da kuma ta ta". Sumayya ta sunkuyar da kanta ƙasa, ƙirjinta na cigaba da bugawa. "Tashi ki je sakatariyata zata sallame ki" Sumayya ta tashi jiki babu ƙwari, ta bar ɗakin, tana tunanin wace masifar suke shirin shiga ita da Nabila. Allah wadaran bakin Nabila da bashi da saiti wasu lokutan. Shi kuma yana babban mutum, menene alaƙarsa da wani Viper, wai shi waye ma wannan vipern, da ya fi kuɗi wahalar samu? Tana fita sakatariyar ta miƙe tana murmushi ta ce "Har kun gama?" Sumayya ta ce "Eh" Ta miƙa mata envelope ta ce "Ga wannan ya ce "A baki" Sumayya ta karɓa ta duba, kuɗi ne maƙudai a ciki, gabanta ya faɗi, tabbas idan ta karɓi kuɗin nan, ta tabatta sai ta din ga bin umarninsa, gashi ba ta san wane irin umarni za a bata ba. Ajiye envelope ɗin ta yi ta ce "Ba na so" Ta nufi hanyar fita, tana tuna yadda ya kirata da wulaƙantacciya. Tana gaggawa ta kai ga ƙofar da zata fitar da ita waje, mutumin da ya karɓi wayarta ɗazu, ya sha gabanta, wanda hakan ya tilasta mata tsayawa. Ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Kamar yadda honorable ya gaya miki, ke zaki yi mana aiki a zahiri, bama buƙatar ta san kina yi mana aiki, dan haka ko kin karɓi kuɗi, ko baki karɓa ba, baki da zaɓi dole sai kin yi komai kasadarsa, ko da kuwa yana nufin sanya rayuwar ƙawarki a siraɗin rasa ranta, zamu yi amfani da ita, idan kuma kin zaɓeta zaki iya rasa taki rayuwar" Cikin matsananciyar damuwa Sumayya ta ce "Muna mata, menene alaƙarmu da ƴan daba, wannan ba aikin hukuma bane ba?" Yayi murmushi ya ce "Shi zaki gayawa hakan ai tun a ciki, idan kuma zaki kai wa hukumar ne, ga fili ga mai doki" Wani abu mai ɗaci, ya tokarewa sumayya a ƙirji. Cikin ɓacin rai ta ce "Amma dai ba ku yi mana adalci ba, wannan tamkar rusa mana rayuwa ne, tayaya muna ƴaƴa mata zaku yi tarkon kama mutum mai irin wannan hatsarin da mu" "Ai ba ke aka ce ba, ƙawarki aka ce, dan haka ina kina son lafiyarki, da mutuncinki, kiyi abun da aka umarce ki, ita ranar biyan buƙata, rai ba a bakin komai yake ba. Ki yi ta kanki kawai, idan har ki ka yi abun da aka buƙata, babu wata alfarma da zaki nema a ƙasar nan ki kasa samu, zaki zama ɗaya daga cikin yaran honorable, za ki yi kuɗi, zaki ɗaukaka za kuma ki shahara, ki nutsu ki yi tunani da kyau, kar ki yi wawanci, ki je aikinki ya fara daga yanzu" Shiru ta yi tana kallonsa, har ya gama maganganun da zai yi, sai dai gaba ɗaya ta rasa wani tunani ma yakamata ta yi. Ba ga ce uffan ba, ta raɓa shi ta buɗe ƙofar ta fice. A cikin mota, direban gidan radiyon, da wanda suka rakota suke tambayarta, yaya program ɗin ya kasance?. Cike da basarwa ta ce musu lafiya ƙalau. Kafin su ƙarasa gidan radiyon, ta ce su sauketa, tana da uzuri, dan haka ta sauka, ta kira Nabila a waya. Tana kira Nabila ta ɗaga, "Yaya kina ina ne? Kina asibitin ko kin tafi gida?" Nabila ta ce "Ina can, wai sai bayan 2-5hrs za su sallame ni, idan na zama stable, haryanzu numfashi yana bani wahala" "Ok to gani nan zuwa" "To masoyiyya Allah ya kawo ki lafiya" Sumayya ta sauke wayar, kamar ta fashe da kuka, duk yadda take da Nabila, ace ta ha'inceta, ta saka rayuwarta a hatsari, anya amana ta ce haka kuwa?. A haka ta ƙarasa Asibitin, ta tambayi ɗakin da Nabilan take, aka nuna mata. Nabila na ganinta ta ce "Oyoyo sumyna" Sumayya tayi murmushin yaƙe ta ce "Ya jikin?" "Alhamdilillah da sauƙi" "Baki kira kowa a gida ba, na ganki ke kaɗai?" Nabila ta ce "Rabu da ni, ba wanda na kira, ƙarshe dai walida ko baba magajiya ne za su zo, dama da DSP yana gari ne, to shi ma wai ya tafi workshop ko me oho dai, Abuja ya tafi, dama da zai zo, to sai anty, ni kuma bana son takura musu, sai dai ba yadda na iya, na gaya wa Abba, kar su ji ni shiru. Amma ya na ga kamar kin yi kuka? yaya program ɗin?" Sumayya ta ce "Wani irin kuka ana zaune ƙalau, program lafiya ƙalau, ga recording ɗin ma ban kai ba, na ce bari na zo na  fara ganinki tukuna". Nabila ta haɗe fuska ta ce "Ki gaya mini idan wani abun yayi miki, mu san abun yi, na gaya miki ni gaba ɗaya mutumin nan bai yi mini ba, dai-dai nake da shi idan wani abun yayi miki, in yi fito na fito da shi, sai in da ƙarfina ya ƙare." Sumayya  ta haɗe rai ta ce "Ke da ya yi mini wani abu kya gannin a haka, ba wannan ba, maganar da ki ka gaya mini a waya, da gaske ki ke ko kuwa?" Nabila ta yi murmushi ta ce "Baki yadda ba ko?" "Yaya za ayi na yadda, mutumin da ake ta fafatukar yaya za a kama shi, ki ce mini kin haɗu da shi, kawai in yadda ta yaya?" Nabila ta kaɗa kai ta ce "Kusan watana guda zuwa na biyu ma,  kawai ina fafutukar yaya zan ganshi, na san dama zaki ƙaryata ni, ban gaya miki ba ma balle ki hana ni ko ki yi mini masifa. Amma cikin ikon Allah, viper ya bar mini shaidar da zai tabattar da  ya ganni" Cikin rashin fahimta, sumayya ta ce "Kamar yaya?" Nabila ta ɗaga rigarta, sai ga plasta a gefen cikinta, ta saka hannu ta cire plastan, sai ga rauni a wurin. Sumayya ta waro ido, tare da rufe baki, ta ce "Na shiga uku, Nabila kin haukace ne? Wai dama da gaske ki ke?" Ta saki rigar ta ce "Ai kafin yayi mini haka, rannan karnuka sun kusa yin watanda ta. Sunayya gayen nan ya wuce duk yadda nake tunani, ashe faɗar sunansa ne a baki kawai mai sauƙi, wallahi idanunsa sun kusa sakani fitsari a wando, sumayya yaya zan kwatanta miki yadda yake ne ki gane abun da na gani? Kwarjininsa ya wuce duk yadda zan kwatanta miki, wallahi da ya shaƙe ni, na ɗauka mutuwa na yi" "Har shaƙe ki yayi, kin ga Nabila ki rufa mana asiri, amma yaya aka yi ki ka samu in da yake?" "Na gaya miki kusan watanni biyu kenan ina nemansa, na san idan na gaya miki, hana ni zaki yi, duk ba wannan ne ya dame ni ba, yayi alwashin idan ya sake ganin fuskata, sai ya kashe ni, kuma mummunar kasada na kuma tafkawa Sumayya". "Ta me kuma?! "Wayarsa na sato, kan na taho!". Alhamdilillah, duka duka a nan mu ka kawo ƙarshen free pages, mu kasance a cikin paid pages, domin jin ainihin gundarin labarin *ƘARFE A WUTA*. ₦500 ne kacal ta wannan account ɗin, masu so ta private special group 1k zasu saka a wannan account ɗin. 0009450228 Aisha Adam jaiz bank Ayshercool. 08081012143 14 🔞 *PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143* *Ina masu buƙatar sayen nagartattun kayan magungunan mata, wanda babu cuta ko algus a ciki, ku yi joining link ɗin nan, domin samun nagartattun magungunan mata* https://chat.whatsapp.com/BLqFsnlyNf0B483RhoWq8v Tsoro Nabila ta fara ba wa Sumayya, "Are you serious? Nabila da ya kashe ki fa, ko kuma idan ya biyo ki fa? Meyasa ba kya tausayawa rayuwarki ne?" "Wallahi nima na yi tunanin hakan, amma ranar biyan buƙata rai ba a bakin komai yake ba, ai bai san in da nake ba, yadda zan ba wa DSP wayar nake tunani, ba tare da ya yi mini faɗa a kan dalilin da ya sa na yi ba, ko tuhumata" Ta ciro ƙaramar waya mai madannai, ta miƙawa sumayya, sumayya ta karɓa tana salallami, da sarawa sheɗancin Nabila. Nabila ta ce "Wayar babu caji, sai na je gida zan sakata a caji" tayi maganar tana karɓar wayar, ta sakata a aljihun ƙaramin wandonta na ciki. Ta sauka daga kan gadon, ta ce "Bari na shiga banɗaki na fito, na baki labari" ta sauka ta shiga banɗakin da yake cikin ɗakin. Sumayya tayi ƙuri da ido tana kallon ƙofar da Nabila ta shiga, tana tunanin yadda abubuwa masu karo da juna suka sakata a tsakiya. Wayarta ce ta fara ringing a cikin jakarta, ta ɗaukko taga baƙuwar lamba, ta ɗaga tayi sallama. Muryar namiji ce ya ce "Ya ku ka yi da ita?" Sumayya ta ce "Ita wa?" "Wurin wa ki ka je?" Aka tambayeta. Ta basar ta ce "Wa ke magana?" "Ya zama dole fa ki yi aikin da aka saka ki, ko kina so ko ba kya so, a in da taken nan idan aka so za a iya kasheta, ko a saceta ayi abun da ake so ta yi, yin abun da aka saka ki ne kawai zai tseratar da rayuwar ta. Ta haɗu da shi ko kuwa?" ta sunkuyar da kai ta ce "Wai dan Allah a tunaninka, tayaya mutumin da ƴan sanda ba su kama ba, ita ta haɗu da shi? Ƙarya kawai take yi dan ta raina mini hankali, Nabila tana da yawan wasa wasu lokutan, amma ƙarya take yi" Nabila ce ta fito daga banɗaki, ta ce "Da wani garan ake waya? Ko kin yi sabon kamu ne?" Sumayya ta katse wayar ta ce "Ba wani sabon kamu" "Sumy, ciwon nan na cikina ne yake yi mini zafi fa" Sumayya ta ce "Ai Allah ya ƙara, ni dama shegen duka ya yi miki, ya kakarya ki " "Ta Allah ba taki ba muguwa, wallahi sumayya da dukana yayi, zai iya kashe ni, kin ga ƙirarsa kuwa, kin ga tsawonsa?. Kin ga a yadda ya din ga kallona, na kasa gane wane irin kallo yake yi mini" Ta kashingiɗe kanta tana gwadawa Sumayya irin kallon da yake yi mata. "Wallahi sumayya ban taɓa ganin ido mai ban tsoron nasa ba, kin ji muryarsa, daga cikin ƙirjinsa yake fitar da ita, abun tsoro, ya ci sunansa viper". Wayar sumayya ta fara vibrating, ta tashi tsaye ta ce "Ina zuwa" Ta fita waje ta ɗaga wayar ta ce "Ya aka yi kuma?" "Idan har ba ta haɗu da shi ba, meye dalilinta na gaya miki ta haɗu da shi?" Kamar sumayya za ta yi kuka ta ce "Yayanta ɗan sanda ne, na gaya muku, a bakinsa da kafafen watsa labarai kawai take jin sunansa" katse wayar aka yi, ba tare da an sake ce mata komai ba. Ta koma ɗakin da Nabila take, sai dai abun mamaki taga Nabilan kamar matacciya. Da sauri ta ƙarasa ta taɓa ta, ta ga bacci kawai take yi, daga fitarta zuwa yanzu bai ci ace har ta yi wannan baccin ba. Message aka turo mata "Idan ki ka bamu bayanin da yake saɓanin gaskiya, abun zai wuce haka, ya zama dole ki bi duk wani umarni da zamu baki, muna bibiyarku daga ke har ita" Sumayya ta ajiye wayar, ta dafe kanta tana salati. Tsaye yake ƙyam a kan ƙololuwar dutsen, yana kallon yadda rana ta doshi faɗuwa, gari ya fara duhu sosai, a hankali ya ɗago hannunsa, ya kalli inhaler da take hannunsa, seretide inhaler ya din ga jujjuyata, yana sauke ajiyar zuciya. "Boss" ya ji muryar Walid a bayansa. Ya zagaya gabansa ya ce "Ka saukko haka dan Allah, magana nake son mu yi" "Bana buƙata kowace iri ce" "Na san na yi maka laifi, amma ka yi haƙuri, zan nemota duk in da take, kuma zan dawo maka da wayarka ina mai baka haƙuri" Ko motsawa bai yi ba, balle walid ya saka ran zai yi magana, daga bisani ya goya hannayensa a bayansa, ya cigaba da kallon rana. "Amma me ka ke tunani game da yarinyar nan? Anya babu wani abu a ƙasa da yakamata mu sani?" A hankali ya juyo, ya dafa kafaɗar Walid, ya matsa da ƙarfi ya ce "Hakan bai dame ni ba, koma wacece, Ma'aruf , madaki, da kuma wannan yarinyar da ka kawo, sai na tabattar da na kashe su gaba ɗaya, ko ta halin ƙaƙa". "A'a master, mace ce, wataƙila sakata aka yi, dan Allah ka yi haƙuri, zan yi maka bincike a kanta " "Idan ka kuma gaya mini wannan sunan, zan hankaɗaka daga kan dutsen nan" Walid ya yi murmushi ya ce "Baka girmama sunan ne viper, idan har ka damu har haka, yakamata ka bawa kanka da lafiyarka kulawa, ta haka ne zaka yi abun da ka ke so, yanzu ka taimaka ka sakar mini kafaɗata, wallahi kamar na karye" Ƙurawa walid ido yayi, Walid ya sunkuyar da kansa, ya san ya tunzuro zuciyar Viper, sakar masa kafaɗarsa ya wuce shi, ya fara sauka daga kan dutsen. Har bayan azahar Nabila ba ta farka ba, su kansu ma'aikatan asibitin, sun yi mamakin irin baccin da Nabila take yi. Hankalin sumayya kuwa yayi mummunan tashi, ganin Nabila ba ta farka ba. Bayan la'asar sai ga Abba, tare da Salim, wanda ƙani ne ga Nasir. A ɗakin da Nabila take suka tarar da Sumayya. Sumayya ta gaishe su, Abba ya amsa ya ce "Sumayya ke ce a wurinta?" Ta jinjina kai ta ce "Eh Abba" "Ai ni ce mini tayi, ba wani abun damuwa bane, ana gama yi mata abun da za ayi mata, za ta koma gida, sai da na koma na tarar ba ta dawo ba" Sumayya ta ce "Eh, ai ta samu bacci ma". Idonsa ya sauka a kan gefen rigarta, da take a huje ga jini, cikin mamaki ya ce "Ya nake ganin jini a jikinta?" Da sauri Sumayya ta ce "amm, dama wai faɗuwa suka a adaidaita sahu, shi ne ta ji rauni" "Amma ni bata gaya mini haka ba ai" yayi maganar cikin matsananciyar damuwa. Wata irin miƙa Nabila ta yi, tare da yin salati, duk suka yi kanta suna yi mata sannu. Suka din ga jera mata sannu, suna yi mata ya jiki. Sumayya ta kirawo likkta, ya zo ya ƙara duba Nabila, yayi rubuce-rubuce a file ɗin ta, ya sallame ta. Abba ya din ga yi mata faɗan meyasa ba ta gaya masa ta faɗi a adaidaita sahu ba, ta nunawa likitoci ciwon da ta ji. Sumayya ta kalleta, suka haɗa ido, sai ta fahimta, dan haka ta ce "Ai ba wani ciwo bane Abba, mu tafi gida na gaji". "Kin tabattar babu wani abu da yake yi miki ciwo?" Ta jinjina kai alamar eh, suka fito zuwa motar Abba, suka tafi tare da sumayya, su ajiyeta a gida. Sumayya ta kalli Nabila ta ce "Wai ya aka yi ɗazu daga fita ta, ki ka fara bacci, kusan awa huɗu ki na bacci?" Nabila ta ɗan yi shiru tana tunani, ta ce "Wani likita ne ya shigo yayi mini allura" "Ba Nurse ba, likita da kansa?" Nabila ta jinjina kai alamar eh, Sumayya ta yi shiru ba ta ce komai ba, a zuciyarta, take jinjina tsagwaron rashin imanin honorable Indabo, kenan idan ba ta yi abun da suke so ba, za su kashe Nabila kenan. Gabanta ya faɗi, ta kalli Nabila da ta kashingiɗa, tana ta lumshe ido, alamar baccin bai isheta ba. Tunani take da wa zata tattauna wannan maganar ne? ko wurin hukuma ta kai, ba ta da shaida ta zahiri, kuma ta san babu wani mataki da za a iya ɗauka a kai. *** Yana kwance a kan gadonsa yana kaɗa ƙafa, hannunsa ɗaya yana riƙe da waya, ɗaya kuma kan shisha, yana ta fesar da hayaƙi. "Hello" sautin muryar mace ya fito daga cikin wayar. Ya ce "Hello, how far?" Ta amsa da "Ya aka yi?" "Mun yi magana da tsoho, ashe kin gano in da yarinyar nan take?" "Eh, na gano, sai dai sun ce ba za su karɓi kuɗi ba, hakkinsu suke nema, dan haka sai ka san yadda zaka yi" Yayi murmushi ya ce "Ki san yadda za ki yi dai, ai kin san dolenki ki ɓoye laifin nan ma, kamar yadda ki ka saba". Cikin takaici ta ce "Ka ce dole?" "Ƙwarai dole, idan asirinmu ya tonu ai kema naki ya tonu, yanzu wane matakin ki ka ɗauka?". Tayi ajiyar zuciya ta ce "Yadda na lura, takamaimai, ba su san waye kai ba, daga ita bar babarta, dan haka zan je gidan ita Antyn taka, a bamu adress ɗin maigadin da suka kaita Asibiti lokacin da abun ya faru, duk da Yallaɓai ya gaya mini, an sallame shi daga aiki, amma dole za mu yi framing ɗin sa da laifin, in case wani zai tayar da maganar, sai mu ce mai laifin ya shiga hannu, abun da nake ƙoƙarin yi kenan" Ya kwashe da wata irin dariya ya ce "Daɗi na da ke akwai brain, anyway ina ne gidan su yarinyar, she needs to learn a lesson, da ita da babarta da ɗan jaridar da ya saka zancen". Da sauri ta ce "Kar ka kuskura, ba zaka ɓata mini aiki ba, na gaya maka ba su san kai waye ba, idan kuma ka yi wani yinƙuri, da ya samar da wata ɓaraka babu ruwana a ciki na gaya maka" Abdul ya ce "Na ji, ina son ganin yarinyar ne kawai" "Abdul, ina da abubuwan yi da yawa a gabana" "Naja'atu, kar ki katse mini waya, ki bani adress ɗin yarinyar". Kashe wayar ta yi, tare da jan tsaki, ta cigaba da rubuce-rubucenta. Nabila sai wajen sha ɗaya saura na dare, sannan ta ɗan dawo dai-dai, sai a lokacin ta samu ta yi wanka, a cikin ɗakinta ta tsaya tana kallon cikinta, da ciwonta, da haryanzu yake yi mata zafi. A haka ta lallaɓa, tayi shafe-shafen skin routine ɗin ta, ta fita kitchen ta haɗo tea, ta dafa indomie, ta koma ɗakinta, ta saka wayar Viper a caji. Ta ɗauki wayarta ta tarar da tarin missed calls ɗin Nasir, ta kira shi ta saka wayar a hansfree, tare da kashingiɗa. Ya ɗaga tare da yin sallama, ta amsa masa a hankali. "Arfa ko ki neme ni, ki ji ya na sauka ko?" A shagwaɓe ta ce "Am sorry, i got a little accident ne, a asibiti na wuni" A ɗan rikice ya ce "Subhanallah, garin yaya meyafaru?" "Don't mind, akwai labari ne" "Wane irin labari? Amma dai kina lafiya ko?" Tayi murmushi ta ce "Gashi muna magana da kai, lafiya ƙalau nake, ka ce Viper daga prison aka sake shi ko? Laifin me yayi aka kama shi?" Nasir ya ce "Ohhh my God, meyasa ki ka damu da lamarin nan ne har haka Arfa?" "Ni ka amsa mini Please" Ya ce "Yeah, amma ya shiga prsion, ba sau ɗaya ba, ba sau biyu ba, shigarsa na ƙarshe ne, ya ɗan daɗe, kuma da alama laifin da ya yi babba ne, sai dai ba wannan ne a gabana ba, kama shi nake son yi. Akwai jami'anmu suna yawo a farin kaya, suna neman bayanai a kansa" "Ka daina wahalar da kanka, na samo maka abubuwan da za su sauƙaƙa maka komai" Ƙasa-ƙasa yayi da murya ya ce "What do you mean? Ba na son wasa fa". Ɗan shiru ta yi, ta tabattar idan ta gaya masa gaskiya a yanzu, ba gwaninta za ta yi masa ba, dan muddin ta gaya masa ta san in da yake, zai ce ta je wurin ƴan daba, zaneta zai yi, kuma sai ya gaya wa Abba ta shiga uku. Dan haka ta ce "Da gaske nake, na je wurin wata client ɗin mu, a unguwar da yake, na samo labari, yana da yaransa da suke ƙananan dilallan tabar wiwi, amma ba su san in da yake ba, wai akwai wani guda ɗaya a tal'udu, yana sayar da katin waya bayan magariba, amma ƙwayoyi yake sayarwa, ya san in da yake". Ya ce "Look arfa, ba na son wasa, daga zuwa unguwar wurin client, har ki ka samu wannan rahotannin?" "Haba DSP, kar ka manta ni ma fa ma'aikaciya ce, wallahi ba ƙarya nake yi ba, daga majiya mai ƙarfi na ji labarin, na je wurin kuma na ga mutumin yana zaman sayar da katin wayar, idan baka yarda ba, idan ka dawo da kanka ka bincika" Yayi ajiyar zuciya ya ce "No, ba sai na dawo ba, zan aika a bincika mini, ina fatan baki gaya wa kowa ba?" "No, babu wanda na gayawa" Nasir ya ce "Good, amma kar ki kuskura ki yi wani abu, da zaki saka kanki a cikin hatsari kin ji ko?" Nabila ta ce "To, idan ka dawo zan baka wani abu mai muhimmancin da zai taimaka maka, amma sai idan zaka yi mini alƙawarin ba zaka dake ni ba, ko ka yi mini faɗa" tayi maganar tana kallon wayar Viper. "Menene abun?" "Sai ka dawo tukuna zan gaya maka, take care" "Shikenan, Allah ya kaimu na dawo ɗin, ki kwanta ki huta" "Ok bye-bye" ta kashe wayar ta ajiye, ta ɗauki ta Viper, da ta yi caji, ta kunna ta. Ta kai wayar hancinta ta sinsuna, ga warin sigari tana yi, ga ƙamshin turare. Ta fara shige-shige a wayar. Cikin call log ɗin sa ta duba, ga lambobi nan, sai dai duk kiransa ake yi ba ya kira, sai jerin private number da ake kiransa da ita. Ta duba cikin messages ɗin sa, babu komai a ciki, sai dai a cikin drafts ɗin sa, yayi saving ɗin wasu kwanakin wata. Tayi shiru tana tunanin yadda ta ɗaukko wayar ta sa, lokacin da take tattare kayan jakarta, da ta buɗe idonta ta gansu a tarwatse, ta ga wayar a gefe, ta haɗa da ita tana sane. Tayi ajiyar zuciya ta ce "Wani laifi ka yi aka kama ka, sannan aka sake ka, ba bisa ƙa'ida ba? Shi yafi cancanta ma in mayar da hankali in binciko, yadda ana kama ka, zan yi raising case ɗin nima, a hukunta waɗanda suka sake ka" tayi maganar tana sake mayar da wayar ta sa caji. "Ko ban ce na san in da ka ke ba, wayarka zata bawa jami'an tsaron damar nuna in da ka ke". Ta mayar da kwanukan kitchen, ta dawo ɗakin ta rufe ƙofarta ta kashe fitila za ta kwanta, sai dai tana kashe fitilar, sai ta ga kamar Viper ne a tsaye a gabanta, saura ƙiris ta kurma ihu, ta kunna fitilar tana zazzare ido, tana cigaba da ƙarewa ɗakin kallo, zuciyarta na saƙa mata ko ya biyo ta. Da ƙyar ta nufi gadonta ta kwanta, gabanta na faɗuwa, ba tare da ta kashe fitilar ba. Zumbur ta kuma tashi zaune, ta ɗauki wayar ta sa, ta sakata a cikin wardrobe ɗin ta, ta rufe ta ta dawo ta kwanta tana rarraba ido. Sai dai fa fafur ta kasa bacci, tsoro ya baibayeta, mussaman idan ta tuna ya ce idan suka sake haɗuwa sai ya kashe ta, sai yanzu ma ta fara tunanin da yaya zata miƙa wayar nan ga DSP Nasir, dan dolen dole sai ya tuhume ta, to idan ya tuhume ta wace amsar za ta bashi? Yaya aka yi wayar ɗan daba ta zo wurinta?. Sai kuma ta koma tunanin, yaya iyayensa suke ji, sun haifi ɗa ya zame wa mutane masifa a gari?. Tsananin zurfin da tayi a cikin tunani, ya sanya, wani ɓarawon bacci, ya yi awon gaba da ita, sai dai baccin bai je ko ina ba, ta din ga jin numfashi a fuskarta. A hankali ta buɗe idanunta, jin saukar numfashi a fuskarta, sai dai me, tayi tozali da fuskar Viper, ya kafeta da manyan idanunsa da suka yi jawur, dogon karan hancinsa yana taɓa nata, ko ƙiftawa ba ya yi. A firgice ta yi ihu, ta faɗo daga kan gadon, jikinta na wata irin kyarma, tana jejjera numfashi, sai dai ta buge wurin ciwonta, dan har ya fara zubar da jini. Sai da ta ɗago ta sake kallon gadon, sannan ta ga ashe filo ne yake taɓa mata hanci, sai ta ga kamar Viper. Ta rintse idanunta tana addu'a, tare da dafe gefen cikinta da yake ta yi mata zafi. Ɓangaren sumayya ma hakan take, dan kasa bacci tayi, dan ita kwanciyar ma gagararta ta yi, tayi dana sanin sha'awar fara aikin jarida, wace irin masifa ce haka tana zaman zamanta, ana neman mayar da ita ƴar ta'adda, saboda an fi ƙarfin ta. Alwala ta yi, ta tayar da salla, ta din ga addu'a, tana fatan Ubangiji Allah ya tsare su daga sharrin honorable Indabo, mussaman Nabila da ba ta san wainar da ake toyawa ba, gashi a yau kawai an yi wasa da rayuwarta, ba tare da ta san hakan ba, nan gaba ba ta san me za su yi mata ba, kuma ta san muddin ta gaya wa Nabila, akwai ƙura dan za ta iya aikata abun da zai sanadin su rasa rayuwarsu gaba ɗaya. Sai dai tana ta tunanin wace hanya Nabila ta bi ta ga Viper, tun da ta ce sun haɗu to lallai sun haɗu ɗin, hatsabibancin Nabila da taurin kanta, har tsoro yake ba ta. Tun da ta ƙududi aniyar yin sunan nan, idan ba wuƙa ta gani a maƙogwaronta ba, babu lallai ta haƙura. Honorable Ma'aruf ne a tsaye yana ta zazzagawa Abdul masifa kamar zai ari baki, shi kuma sai cika yake yana batsewa yana harare-harare. "Na fara gajiya da rashin mutuncinka Abdul, na gaji, gashi a banza ka nemo magana a wurin ƴar matsiyata, sun ƙi yadda a haɗa kai da su, a binne taiyar da ka shuka, dole sai na ɗau mataki a kai. In the next couple of years, kai zaka tsaya takarar deputy governor a garin nan, kamar yadda muka yi yarjejeniya da party, kafin na shiga, amma sai shashanci ka ke yi, so ka ke yi sai lokacin ya yi ƴan adawa, su ɓata mana shiri, na gaji da zubar da jini, saboda rashin hankalinka da wautarka, na ce ka yi aure ka ƙi, daga shaye-shaye sai neman mata, idan ma zaka yi yakamata ka san abun da ka ke ciki" Abdul ya numfasa ya ce "Ka yi haƙuri, ni yakamata na goge wannan ɓarnar da kaina, ka karɓar mini address ɗin yarinyar, zan san abun yi" "A baka ka je ka kuma yi wa mutane wani shirmen ko?" Ya girgiza kai ya ce "No, na yi maka alƙawarin ba wani shirmen zan yi ba, zan goge komai ne kawai" "Ɓace ka bani wuri" yayi maganar yana hakin baloƙoƙon da ya yi. Nabila fa abu ya zame mata ga ƙoshi, ga kuma kwanan yunwa, wayar Viper ta zame mata larura, ta rasa yadda za ta yi. Da safe Abba ya ce ta zauna a gida ta huta, saboda jikinta, amma ta ce masa ita ta ji sauƙi, fita za ta yi, da kansa ya ɗauke ta a mota, ya tafi kaita wurin aikin, suna tafe yana yi mata nasihohin da ya saba yi mata, amma da za a yankata, ba zata iya faɗar me yake cewa ba. A gate suka haɗu da Director, yana ganin major kamar zai dungura, saboda risunawa cikin girmamawa, ya gaida major. Ya amsa masa cikin girmamawa yana tambayarsa aiki. Director ya amsa da "Aiki Alhamdilillah, yau kuma da kanka ka kawo ta?" Major ya ce "To ya na iya, ƴar gudaliyata babu lafiya, kuma ta dage sai ta fito aiki. Ina fatan dai yanzu tana mayar da ka?" Director yayi murmushi ya ce "Alhamdilillah, ta rage shiririta, tana aiki sosai ranar Alhamis ma za ta fita trial ita ce incharge of case ɗin" Major ya ce "Masha Allah, idan ki ka yi wining, akwai special gift" Tayi murmushi kawai ta sauka daga motar, dan ba wani ganewa take yi ba. A wurin aikin ma, jin ta ta din ga yi tamkar wadda ta shekara tana amai da gudawa, gaba ɗaya gaɓoɓinta a sage suke, da ta motsa, sai ta ga kamar za ta ga Viper a gabanta. Layin Nasir ta kira, tayi sa'a ya ɗaga ya ce "Ya aka yi kuma?" "Ka aika a bincika maka maganar mutumin nan ne?" "Ki kwantar da hankalinki mana, ina sane zan aika". "Ai kar ka zo ka ce ƙarya nake yi ne" "Haba dai ni na isa ma" "Yaya" Ya amsa da "Na'am barrister Nabila maitama". "Wane laifi Viper yayi na ƙarshe ne, aka rufe shi?" "Ban gani ba a cikin record ɗin sa, waɗanda na gani dai, kawai rigima ce da mutane, da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi da kuma dillancin su". "Wace kotu da wace kotu aka taɓa kai shi?". "Arfa ban sani ba wallahi, wai menene akwai matsala ne?" Ta kashingiɗa ta ce "No, babu wani abu sai anjima" Ta kashe wayar ta ajiye, ta tashi ta tafi office ɗin Barrister Habib. Bayan ta yi sallama, ya amsa mata, yana ƙura mata ido, har ta ƙarasa ta zauna. Kai tsaye ya ce "Menene matsalar?" Ta ce "Na yi kama da mai matsala ne?" "Eh mana, yau ba kwalliya, ba ƙwalisa ba biscuit, ba sweet a hannu, duk yau dai sai a hankali" Tayi murmushi ta ce "Barrister ka bani dariya, saka mini ido ka ke yi kenan, ka san jiya a asibiti na wuni, shiyasa ban zo ba jiya" "Eyya, ai na zata mulkin ne ya motsa, ki ka ƙi zuwa, tun da ke ba tuhumarki ake yi ba, ba kya laifi" Sake sunkuyar da kai ta yi tana murmushi. Shi ma murmushin ya yi ya ce "Ina jin ki, meyafaru, dan ba kya zuwa office ɗin nan sai da dalili" Ta gyara zamanta ta ce "Barrister, na san ka san wani ɗan daba da ake nema ko? Aminu Viper" Yayi mata ƙuri da ido yana kallonta. "Dama wani labari na ji, wai wani laifi ya yi aka kai shi prison, kuma kawai sai aka sake shi ba bisa ƙa'ida ba, gashi sai ɓarna yake yi a gari" sai kuma ta yi shiru. Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ina jin ki" "To shi ne, sonake na san wani laifin ya yi, ban sani ba dan Allah ko zaka bincika mini, a wace kotun aka yi masa shari'a" "Meyasa ki ke son sani?" "Eh, sonake idan an kama shi, na bibiyi shari'ar da za ayi masa, kuma na binciki meyasa aka sake shi da" Wata ƴar dariya ya yi ya ce "Nabila kwanan nan na ga you are so much serious, amma kin san hakan kamar tarar aradu da ka ne ko? Amma let's see how far you can go, zan bincika miki in sha Allah, nan da 3days zan neme ki" "Na gode sosai babban yaya, Allah ya ƙare ka, na gode sosai da sosai" Yayi murmushi tare da jinjina mata da hannunsa ya ce "Ki huta little barrister " *** Can gidan su rahama kuwa, ta samu bacci, mamanta na tsakar gida tana ta shara, kasancewar ta mace mai son tsafta, jin motsi a bayanta, ya sanya ta waiwaya domin ta ga abun da yake faruwa. Matasa ne su uku, zabga-zabga cikin shigar banza a tsakiyar tsakar gidan. A tsorace ta ce "Lafiya kuwa? Meyafaru?" Ya ƙarewa gidan kallo ya ce "Dama a nan ku ke rayuwa, ƙasƙantattun matsiyata, amma har ki ke fatan ganin an kai ni kotu an karɓowa ƴar ki hakkinta? Har wani hakki ne da ita? Talaka yana da wani hakki ne ko ƴanci?" Cikin rawar baki ta ce "Waye kai malam?" "Na yi miki kama da malam? Ni na yi wa ƴar ki fyaɗe, da ki ka tafi nema mata hakkinta?". Sakin tsintsiyar ta yi, tana kallonsa, a ƙalla zai kai shekaru talatin da takwas, kallon idonsa ta yi babu mutunci ko imani a cikin su. "Yanzu kai ka iya samun ƙwarin gwiwar zuwa gabana, ka gaya mini ka yi wa ƴa ta fyaɗe? Bayan ka turo mini waccan bayahudiyar ta yaudaremu, ba ta yi nasara ba, shi ne ka zo gabana ka gaya mini ka keta wa ƴa ta haddi?" Ya fara takowa gabanta ya ce "Yes, na zo na ƙara kashe ƙishirwa ta ne, sannan in yaba wa baiwar Allah da Allah ya yi wa ƴar ki, kin iya haihuwa" Yayi maganar yana wata irin dariya, a fuskar maman rahama, da tuni idonta ya fara zubar da hawaye. Ya saka hannu ya riƙe ɗan kwalin kanta, haɗe da gashin kanta, ya tsuke fuska ya ce "Kin san ko ni waye, da ki ka saka na tako ƙafata wannan ƙazamin kucakin ƙauyen" Ihu ta saki, saboda zafi. Salim ya ce "Kai Abdul wannan yawa ne fa, ba wurinta mu ka zo ba fa" "Bar ni Salim, duk da hausawa sun ce abun cikin ƙwai, ya fi ƙwai daɗi, what if na wajen ƙwan ya fi?" Yayi maganar yana riƙe rigarta. Salim ya ce "No, kar ka yi haka, akuyanci kenan ai, dan Allah ka bari" Abdul zai yi magana, suka yi ido huɗu da rahama, a tsaye a ƙofar ɗakin su, tana kallonsa. Ayshercool 08081012143 15 🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143* *Ina masu buƙatar sayen nagartattun kayan magungunan mata, wanda babu cuta ko algus a ciki, ku yi joining link ɗin nan, domin samun nagartattun magungunan mata* https://chat.whatsapp.com/BLqFsnlyNf0B483RhoWq8v 15 A take ya hankaɗe uwar a gefe, ya yi wa ramma wani irin miskilin murmushi, ya nufe ta yana wata irin tafiya, irin ta riƙaƙƙun ƴan iska ya ce "Hi baby girl, long time almost 2months kenan fa ko?" Hawaye ne ya fara bin fuskar ramma, jikinta ya hau rawa. Ya sanya hannu ya dafa jikin bango, yana ƙare mata kallo ya shafi sumarsa ya ce "To ya ki ke, kin warke?" Shiru ta yi ta sunkuyar da kai, tana tuna waccan ranar, da irin yadda ya keta mata haddi cike da zalunci. Ya ce "Ohh, wai waccan ranar ce haryanzu ba ki manta ba ki ke kuka? Ya wuce ai wancan, kin bar ni da tsananin kewarki, duk ruwan da na sha komai sanyin sa, ya daina kashe mini ƙishirwa". Ya kai hannu ya ɗago fuskarta, ya shafi hawayen da suke ta ambaliya a kan fuskarta. Yinƙurawa mamanta ta yi da sauri, tana kururuwa ta ce "Kar ka taɓa mini ƴa, mugu azzalumi, wai babu wanda zai kawo mini ɗauki ne?" Ya kalli su Salim ya ce "Ku saka mini matar nan a silent" Haka suka rirriƙeta, suka ɗaure mata baki, suka shaƙa mata wani abu, a take jikinta yayi laƙwas. Ya sake kallon ramma ya ce "An ce akwai unborn ɗi na a cikin ki ko? da gaske za ki haife shi kuma?" Cikin kuka ta ce "Ban yafe maka ba, ka lalata mini rayuwa, ban sanka ban taɓa ganinka ba, ka biyo ni gida kana wulaƙanta mini uwa, dan bamu da kuɗi, Allah ya saka mini" tayi maganar tana fashewa da kuka iya ƙarfin ta. Salim ya sunkuyar da kai ya yi shiru, haka nan ya ji abun yayi masa wani iri a zuciyarsa, sauran matan da suke lalata da su, suke kai kan su, wannan kuma yarinya ce ƙarama. Dariya ya yi ya ce "Dan kin ce baki yafe ba, ba zai hana ni shiga aljanna ba, kun ƙuduri aniyar neman hakkinku, duk da an yi muku tayin kuɗi kun ƙi, zan nuna muku ƙarfi da izzar kuɗi a ƙasar nan". Ya danƙi hannun ramma, da jikinta ya ɗauki zafi sosai. Tana ihu tana kiran mama, ya ja ta suka fice daga gidan, suka sakata a mota suka tafi da ita. ***** Ɗan mama ne ya shiga ɗakin Viper, ya tarar da shi yana ta sintiri a ɗakin. "Ka daɗe ka yi ƙarko uban gidana" Viper ya tsaya cak, yana jiran ya ji me zai ce. "Na yi aikin da ka saka ni, ya tafi yadda yakamata " Ya kaɗa kai tare da yi masa alamar ya ƙaraso. "Ina labarin malam lawan?" "Kamar dai yadda ka ce, an kula da komai, sai dai babu wanda ya sake zuwa, gashi yanzu yana yawo a cikin unguwa". "Madaki fa?" "Shi ma kamar dai yadda ka sani, Honorable indabo yake yi wa aiki yanzu". "Ina buƙatar isassun kayan aiki, a kwanakin nan zan dirar masa, mu ɓalla ƙarfe, sai dai mu yi mutuwar kasko, ayi wadda za ayi". "Ba yanzu ba" suka ji muryar Walid. Suka mayar da hankalinsu kan sa. Walid ya ce "Viper da sauran lokaci, kai ka san madaki ba haka kurum yake daba ba, da zai kasu cikin sauƙi, da tuni mun kawar maka da shi, ka ɗan saurara tukuna" A hasale ya ce "Ba zan saurara ɗin ba tukuna" "Viper!" Ciki ƙaraji ya ce "Walid ka ƙyale ni" Walid ya girgiza kai ya ce "Da zan iya, da tuni na yi, mutumin nan ya fi ƙarfinmu ko ta ina, idan ka yi amfani da zuciya wallahi ba zamu yi nasara ba, ka bari mu bi komai a hankali mu lissafa, yadda ko mutuwar kasko ce mu yi" Cikin ƙaraji ya ce "Ba zan jira ba, na gaji, na gaya maka na gaji. Na so bin komai a hankali, meyasa ka kawo mini yarinyar saboda me? ka san ka ƙara tunzara zuciyata yaya ka ke so na yi, so ka ke sai na haukace tukuna? Kalli yadda na koma walid, kalle ni, abun da nake ta ƙoƙarin dannewa ka fama mini, dan me zaka kawo mini wannan yarinyar sannan ka ce na nutsu how? Ta ɗauki wayata ta tafi, ka na da tabbacin hannun wa wayata za ta shiga? Idan aka tashi kama ni, kana da tabbacin su waye za su kama ni, idan na ƙare a haka ban aikata abun da nake ƙuduri ba fa? Ko dai ka nemo duk in da yarinyar nan take na kasheta, ko kuma a yau ba sai gobe ba, sai na yi gaba da gaba da madaki ko na kashe shi ko ya kashe ni, amma kafin nan sai na fara gaba da gaba da wancan dabban" tuni gumi ya tsatsttsafo masa, jijiyoyin kansa suka mimmiƙe, kafofin gashinsa ya bubbuɗe. Walid ya taka gabansa a hankali, cike da shirin ko ta kwana, dan ya san ƙarshenta sai ya ba shi gwale-gwale, ko ya mangare shi. Ya shammace shi, ya soka masa sirinji a damtsensa, kasancewar jikinsa babu riga, ya fara yi masa allura, sannan ya fara yi masa magana. Walid ya ce "Na san na yi laifi, amma ka bari na gyara laifina da kaina, na san abun da ka ke ji ɗan uwa, ba kai kaɗai ka ke ji ba Al'amin" Viper ya zubawa walid ido, ya rasa me zai yi, yana tsaye ya kashe masa jiki, ba zai iya komai ba, kasa tsayuwar yayi, ya tafi zai faɗi walid ya riƙe shi ya kwantar, ɗan mama kuwa dama tuni ya arce, dan yana tsoron a shaƙe shi. Barrister Naja'atu ce zaune a katafaren ofishin ta, tamkar na matar gwamna, yana ɗauke da duk wani kayan alatu da ake buƙata. Sannu a hankali take shafa screen ɗin wayarta, daga bisani ta saka wayar a kunnenta. "Honorable, ka isa Abujan ne?". Ya amsa da "Eh ma sauka" "Ok, yaya maganar yarinyar nan da Abdul ya yi raping?" "Yes, he handle the case himself, yayi maganin abun". Ta ce "Ok, ina fatan ka ja masa kunne, kar ya je ya aikata wani shirmen da ba zamu iya gyarawa ba". Ya ce "No, kar ki damu, zai yi abun da ya dace". Tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, dama ina tsoron ya yi wani shirmen ne, amma tun da ka ce haka, shikenan" Ta katse wayar, ta mayar da hankalinta kan sakatariyarta da ta shigo. Cikin gyatsine ta ce "Ke kuma ya aka yi?" "Kin yi baƙi ne ma" "Suwaye?" "Eh to, da alama dai ƙorafi suka kawo, ke suke..... "Ke bani da lokaci, ayyuka sun yi mini yawa, su ganki ko wani daban, hutawa nake buƙata, wannan jaraba a uzzurawa rayuwarka, london zan wuce ma ni this week na je na huta. Ki fita ki je ki sallame su" ta juya jiki a sanyaye ta bar office ɗin. Salim ya kalli Abdul da ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, yana shan giya a cikin wine cup ya ce "To wai yanzu ya zaka yi da yarinyar nan da ka kawo ka ajiye, Ga abun da aka tsara, kai kuma ga abun da ka yi?" Ya ɗan girgiza giyar a cikin kofin sannan ya ce "Gani na yi za ta ci bulus idan ta tafi a haka, sai na gama moreta zan aikata kawai" "Amma ba ka ganin, hakan zai iya kawo matsala, yanzu ko a nan gaba?" Ya girgiza kai ya ce "Ba wata matsala, na ɗan lokaci ne, zan gama abun da zan yi da ita, zaka iya tafiya ma kawai" Ya jinjina kai ya ce "To shikenan" Sannu a hankali ta buɗe idonta, ta din ga gani dishi-dishi, ta kasa tantance a ina take, dan ba ta taɓa ganin wurin ba. Ji ta yi an rufe ƙofa, ta ɗaga kai ta kalli mai shigowar, take gabanta yayi mummunar faɗuwa, duk da idonta bai gama washewa ba, amma sarai ta gane shi. "Kin tashi kenan? abun da aka shaƙa miki bai taka kara ya karya ba, amma ki ka yi wannan dogon zangon" yayi maganar lokacin da ya tsuguna a gabanta yana kallon idonta. Ƙirjinta ya din ga bugawa da sauri da sauri. Ganin ba ta ce komai ba, ya sanya ya tashi ya fita, babu jimawa ya dawo da plate a hannunsa, ɗauke da indomie da kifi a ciki, sai ruwan roba, hannunsa ɗaya kuma ledar magunguna ce. Ya tura mata plate ɗin gabanta, sannan ya fara haɗa alluran. Tayi shiru ta zuba masa ido, har sai da ya ce "Ki ci mana, allura zan yi miki" Cikin kuka ta ce "Dan Allah kar ka kashe ni" Abdul ya yi wani murmushi ya ce "Saboda me?" "Ni dai kar ka kashe ni, dan Allah ka mayar da ni wurin babata" Ya kalleta ya ce "Kashe ki fa sai na yi, ba dai ke taurin kai ba ke da babar taki, zan nuna muku cewa talaka ba komai bane illa bawa kuma takalmi ga masu kuɗi da dukiya, ba yanzu zan kashe ki ba, sai kin gama yi mini amfani tukuna. Yanzu ki ci abincin nan, zan yi miki allurai na zazzaɓin da yake jikinki". "Ni ba zan ci ba" ta yi maganar za ta tashi tsaye, amma ya daka mata tsawa ya ce "Wallahi idan ba ki ci ba, a yanzu zan kashe ki, ko gawarki babarki ba zata gani ba". Babu shiri ta fara cin abincin, sai dai a loma ta uku, ta hau amai, ta amayar da duk abun da ta ci. Cikin tsananin takaici ya ce "Ke mahaukaciyar ina ce zaki yi mini amai a nan? Nan yayi miki kama da wurin juye ƙazanta?. Tayi shiru ta sunkuyar da kai. "Tashi mu je in nuna miki in da duster da mopper suke ki gyara" Cikin tsoro ta tashi, tana jiri tana bin bango, haka ya saka ta gyara wurin da ta yi aman. Bayan ta gyara, ta shiga banɗakin tayi alwala, ta fito ta tayar da salla, ba tare da ta san ina ne gabas ba, da kuma adadin sallolin da ake bin ta ba, dan ba ta san adadin lokacin da ta shafe, ba a hayyacinta ba. Ya dawo ya tarar da ita a zaune, a takure wuri guda, bai kulata ba, ya ƙarasa ya sanya hannun sa a goshinta, ya ji shi da zafi rai. ɗaga ta ya ja ta ya dungurar da ita a kan gadon. Ya kama hannunta, ya saka sirinji, ya fara ɗaukar jininta. Bayan ya gama ɗaukar jininta, ya yi mata wasu allaurai duk a jijiyar hannunta. Ta zubawa saurautar Allah ido, dan kasa magana ta yi, tun yana allurar ta fara jiran jin alamar ciwonta ya ƙaru, dan ta sallama kashetan zai yi kamar yadda ya faɗa, amma bayan ya gama yi mata ya tashi ya fice, ya kulleta a ɗakin, ba tare da ta ji yanayinta ya sauya ba. *** Abun duniya fa ya ishi Nabila, wayar Viper ta zame mata wahala, dan kuwa kashe ta tayi gabaki ɗaya, sai dai duk in da ta zauna, musamman da daddare, idan ta shiga cikin duhu, Viper ne yake yi mata gizo, har abun ya fara tasiri a yanayin mu'amalarta. Tana toilet tana wanka, wayarta ta din ga ringing babu ƙaƙƙautawa, ta kammala wankan ta fito, ta ɗauki wayar tana dubawa. Lambar Nasir ta fara kira, ta nemi wuri ta zauna a gefen gado, tana jiran ya ɗaga. "Ina ki ka shiga ne? Ko kina wurin aiki ne?" Ta ce "A'a, yanzun nan na dawo gida" "Baki da lafiya ne?" "No, gajiyar aiki ce kawai" "To, aikin ki yayi kyau arfa, na yi waya da mu'azzam, gayen nan da ki ka faɗa mun kama shi, tare da tabar wiwi da ƙwayoyi" Sassanyar ajiyar zuciya ta yi ta ce "Alhamdilillah ala kulli halin, Allah shi ne abun godiya, what next?" Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Na saka lallai su fara tuhumarsa, ya faɗi in da Viper yake". Zuciyarta ta din ga raya mata ko ta sanar masa kai tsaye, abubuwan da suke gudana, ta bashi wayar hankalinta ya kwanta, amma zuciyarta ta gargaɗe ta a kan aikata hakan. *** In da ya bar ta a kan gadon, nan ya je ya sake tarar da ita, ta tashi ta zauna ta dunƙule jikinta a wuri ɗaya tana bacci, sai ajiyar zuciya take yi. Wani irin murmushi ya yi, yayi miƙa lokaci guda, ya fara rage kayan jikinsa. Motsinsa ya sanya ta farka, fes ta buɗe idanunta, sai dai hankalinta ya yi mummunan tashi, ta ja da baya, ba ta ƙaunar ganinsa ko kaɗan. Ya hawo kan gadon ya nufota, ta din ga ihu tana kiran sunan Allah, ta na yi masa magiyar ya ƙyaleta, ya mayar da ita gida. Amma kamar ya kamo ƴar kaza, haka ya danƙota zai yi mata rashin mutunci, sai dai yana haɗa ta da jikinsa, ya ji kamar ana hura wuta a Jikinta, saboda zafin zazzaɓi, gashi sai wani irin ƙarni take yi, da warin man kaɗanya da take shafawa ya haɗe da ƙarnin koren sabulun da take wanka da wanki da shi. Ba wannan ya fi damunsa ba, rashin saukar zazzaɓin jikinta ne bai so ba, dan ko a yanzu a galabaice take. A ɓangaren ramma ma, warin giyar da yake yi, da ƙamshin turaren sa ya sanya ta fara yinƙurin amai, ba shiri ya cikata, ta sauka da gudu, ta tafi banɗakin da yake cikin ɗakin, ta din ga kwara aman, sai dai ruwa kawai take amayarwa, bayan shi babu komai a cikinta. Ta gama aman tana ta sauke numfashi, ta lallaɓa ta fito, tana bin bango, sai dai ta tsaya cak tana kallon sa yadda ya zuba mata ido. Cikin kuka ta haɗa hannayenta ta ce "Dan girman Allah ka yi haƙuri, ka mayar da ni in da ka ɗauko ni, hankalin mamana na san yana can a tashe, dan Allah ka yi mini rai ka yi haƙuri" ta ƙarasa maganar tana zubewa a kan gwiwoyinta tana bashi haƙuri". Strip ɗin gwajin ciki ya ɗago da yake hannunsa, wanda ya gwada da jininta da ya ɗiba ɗazu ya ce "Ke ce mace ta farko da ta fara ɗaukar cikina, kin kafa tarihi, tun da ki ka ce ba za a zubar ba, nima na ji ya shiga raina, ina son abuna, zaki haife shi kafin na kashe ki, kuma ba zan kashe ki ba sai bayan kin haihu" ta yi shiru tana cigaba da zubar da hawaye, wai ita ce ɗauke da ɗan shege a cikinta, a wani keɓantaccen wuri tare da ɗan iska, saboda kawai ba su da kuɗi, sai yau ta ƙara tabattar da illar talauci. Ya miƙe tsam daga kan gadon ya fice ya bar ta a ɗakin, ba tare da sanin makama ko abun yi ba. Sumayya ce a office ɗin manager, fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa. Ya kalleta ya ce "Sumayya yaya aka yi ne? Ko yayi miki wani abun ranar da ku ka yi program ɗin?" Ta girgiza kai alamar a'a. "To menene? Na ga kin yi editing ma kin tura mini, komai yayi normal, na ce a saka idan lokaci yayi kin yi ƙoƙari sosai, ina ga program ɗin hannunki zai dawo gaba ɗaya" Ta sauke numfashi ta ce "Sir" Ya amsa da "Yes ma" Sai kuma ta yi shiru. "Ki gaya mini mana idan da wani abu" ta girgiza kai ta tashi ta fita. Addu'a ya din ga yi a zuciyarsa, tare da fatan Allah ya sa ba wani abun indabo yayi mata ba, dan ya san halinsa sarai. Nabila tana office ɗin ta, tana aiki, barrister Habib ya buɗe ya shiga da sallama. Miƙewa tayi tsaye ta ce "Sannu da zuwa, da ka kirawo ni ai" Ya ƙarasa gaban teburinta ya ce "Babu damuwa, aikin da ki ka ba ni ne na yi" Tayi murmushi ta ce "Taimakon da na nema dai aka yi mini" Shi ma murmushin ya yi ya ce "Zan tura miki court ɗin da aka fara yi masa shari'a, da sunan wurin wanda za ki je ya binciko miki file ɗin, akwai dai wani abu a ɓoye". Cikin sauri ta ce "Ok, ai daga nan ma kana tura mini sai na tafi" Ya ce "Wait, ki tafi yanzu ba ki da aiki ne?" "Ai na kusa kammalawa saura kaɗan ne" Ya ce "shikenan, zan tura miki ta what's app, amma ki bi a hankali, fa kar ki je ki yi abun da ba shikenan ba" "In sha Allah, na gode sosai" Yana fita ta fara lissafi a ranta, tun kan viper ya je hannu, za ta bibiyi cases ɗin sa na baya, domin a shirye take da ta ƙalubalanci hukumar shari'a ciki har da alƙall da kuma hukumar gidan yari, kan sakin Viper ba tare da ƙa'ida ba, ta san ko ba ta yi nasara ba, za ta yi suna sosai. Tattara jakarta ta yi, ta fita bayan da saƙon barrister Habib ya shiga wayarta. Ba ta wani sha wahala ba zuwa kotun da ya bata adress ɗin, tun da dama sananniyar magistrate court ce a kano. Ofishin rijistra ta je, suka gaisa da mutanen wurin, sannan ta tambayi office ɗin mutumin da barrister Habib ya gaya mata. Aka yi mata iso, sannan ta gabatarwa da mutumin kanta, da wanda ya turo ta. Ya karɓeta da mutuntawa sannan ya ce "Baiwar Allah, gaskiya ta in da ki ka biyo, babu yadda za ayi na kasa yi miki alfarma, amma riƙe file ɗin nan, tamkar saka hannu ne ki ɗaukko ƙarfen da yake cikin wuta ne, dan Allah kar ki je ki yi wani abu da bai kamata ba, tun kan ki zo aka yi waya, aka ce a baki idan kin zo" Nabila ta ce "In sha Allah, babu wani abu da zan yi, ina ɗan yi wani bincike ne kawai". Ya ja ta suka tafi wani wuri a cikin kotun, suka shiga can wani office, da ba zaka ce akwai mutane a wurin ba, sai da suka shiga can ciki, suka iske wani mutum yana ta aiki a computer. Suka gaisa, wanda ya rakota ya ce "Oga, ga baƙuwa mun yi, Barrister Habib ne ya aikota, shi kuma daga top oga, ya ce a kawo ta file ɗin Al'amin viper zaka ɗaukko mata" Shiru mutumin yayi yana kallon ta sannan ya ce "Ya sunanki?" "Nabila yusuf maitama" "Me za ki yi da file ɗin?" Ta ɗan rausayar da kai ta ce "Wani bincike nake yi ne" Ya mayar da hankalin sa kan mutumin da ya rakota ya ce "Ka gaya mata illar da ke cikin hakan?" "Na gaya mata, ko ma dai menene na gaya maka wanda ya ce a ba ta ai" Yayi ajiyar zuciya yana cigaba da yi wa Nabila kallon tuhuma, ya tashi ya shiga wani wuri. Ta kalli mutumin da ya rakota ta ce "Yallaɓai, meyasa file ɗin yake da hatsari har haka?" Yayi murmushi ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Yana da alaƙa da rashin gaskiya" Mutumin ya fito ɗauke da file ɗin, duk ya yi ƙura, hannu na rawa ta karɓa ta ja kujera ta zauna, ta fara dubawa. Sannu a hankali ta din ga bin bayanan ciki, da binciken rahoton ƴan sanda a kai, sai dai komai ba straight forward aka yi shi ba, gaba ɗaya kanta ya kulle, ba ta fuskanci wani abun kirki a ciki ba. "Amma sir, ina ƙarshen shari'ar, ai wannan ba a yanke hukunci ba, ranar ƙarshe da aka ɗaga shari'ar an ce sati uku za a sake zama, yanzu kusan shekara biyar, ba a sake rubuta komai ba" Mutumin ya ce "Eh yadda ki ka gani a haka yake" Cike da mamaki ta ce "Dan Allah wane alƙalin ne ya yi masa shari'ar?" "Yana abuja" suka bata amsa a taƙaice. "Wannan documentation ɗin, sam ba a yi shi ma yadda za a fahimta ba, amma dan Allah.... Wanda ya ɗauko mata File ɗin ya ce "Mu fa babu abun da za mu iya sake gaya miki, ba wanda yake da damar zuwa wurin nan sai staff ɗinmu, dan haka ki tashi ki tafi". Ta miƙe tsaye ta ce "Na gode sosai" Ta fito daga office ɗin tana mamaki, ta ja ta tsaya tana kallon office ɗin, a abun da ta fuskanta wuri ne da ake ɓoye files na musamman. "Yayi kisan kai!" Ta faɗa a fili. "Ba abun mamaki bane ba, da gani zai aikata abun da ya fi kisan kai, amma menene dalilin ajiye shi shekara biyar, ba ayi masa shari'a ba, an ɓoye file ɗin sa a wuri na musamman, ya shekara biyar a prison, kuma kwatsam an sake shi, babu document na wanke shi aka yi daga laifin ko kuwa, duk da an rubuta ya amsa laifin, amma wane hukuncin aka yanke masa? Wayyo Allah kaina zai fashe" ta yi maganar tana dafe kanta, da ya yi mata nauyi. *** A tsaye yake a kanta yana ƙare mata kallo, yanayin yadda take a kwance ya tabbatar masa da salla ta yi. Ruwan robar hannunsa ya fara zuba mata a Jikinta, hakan ya razanata ta tashi a gigice. Ya watsa mata sabulu da soso a jiki ya ce "Ki tashi ki je ki yi wanka, ba na son ƙazanta, kar ki haifar mini ɗa mai dauɗa" Ta yinƙura ta tashi da kyar, tana jiri, ga yunwa ga zazzaɓi ga kwana da ta yi amai, ta din ga bin bango, har ta isa banɗaki. Ta daɗe a banɗakin tana kuka, sannan ta yi wankan ta fito, ta tarar da shi a kan gado a zaune yana danna waya. Ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Dalla cire wannan kayan, ƙazamar banza da wofi, har amai ki ka yi a jikin kayan amma ki ka mayar da su jikinki" kallonsa take yi, to tsirara yake son ta zauna? Ya buɗe wardrobe ɗin da ke ɗakin, duk kayansa ne a ciki, ya jefa mata wata shirt, ya ce ta ɗauka ta saka. Banza ta yi masa, ta kawar da kanta gefe, wanda hakan ya hasala shi, yana zuwa gabanta ya kwasheta da mari, abunka da jiki babu ƙwari, take ta faɗi ƙasa, ta riƙe fuskarta. "Ke kin isa ina magana ki yi mini banza, ƴar wahala mara amfani, ɗauki ki saka kan na tattakaki" Ramma ba ta ƙaunar duk da abun da zai taɓa lafiyar jikinta, haka ta zura rigar nan, ta zo mata har gwiwa, sai rufe jikinta take yi. Ya danƙota, ya fita falo da ita. A falon ya haɗa mata baƙin shayi, sai soyayyen dankali da ketchup ya ce ta ci. Gaba ɗaya a tsorace take, saboda kar ya kuma dukanta, haka ta din ga tsakura tana ci tana hawaye. Ta gama ci, ya ɗaukko alluran zazzaɓi da yake yi mata yayi mata. Ta lura yana da mai aiki a gidan namiji, har girki da gyaran gidan shi ne yake yi masa su. Ya kashingiɗa yana kallon tv, ita kuma tana gefensa a ɗarare, sai mutsu-mustu take yi tana share hawaye. Sahidar yatsunsa ya gani kwance a fuskarta, har ya ɗaga ya basar ya cigaba da kallonsa yana kaɗa ƙafa. *** "Allah ya taimaki maigida" "Menene labari?" "Na samu kiran waya ɗazu, wata yarinya ta je an kaita har ofishin secret files, an ɗaukko mata file ɗin viper ta duba" "Wacece ita?" "Yarinyar da ka ce ayi amfani da ita a kama Viper" Da sauri ya ce "What? Ya aka yi ta san da file ɗin ta je? Waye ya ce a bata?" "Wallahi ban sani ba, amma an tabattar mini da ga sama su ma aka ba su umarnin ba ta" "Sama ina, waye ya bayar da umarnin?" "Ban sani ba wallahi, kuma da gaske lawyer ce, idan kuwa haka ne, za ta iya yiwuwa da gaske ta haɗu da Viper, ƴar jaridar nan raina mana hankali ta yi" Indabo ya numfasa ya ce "Kar ku yi gaggawa, kar ta san mu na bibiyarta, ka bi ta hannun ƙawarta, ku samo me take son samu a kansa, idan ta ƙi, ku kamata ku azabtar da ita". Ya amsa da "Ok sir". Daga kotun, gida arfa ta tafi, tun daga shigarta, Sauda ta fara tsokanarta da faɗa, amma ba ta ita take ba, ɗakinta tafi ta cigaba da tunani da lissafi. Kamar wadda aka zungura, ta ɗaukko wayarta ta kira Nasir. Murya ƙasa-ƙasa ya ce "Arfa ya dai? Mun shiga meeting ne" Kamar za ta yi kuka ta ce "Yaushe za ka dawo?" "Zamu yi waya an jima, ki yi haƙuri" "Kar ka kashe mana dan Allah, ni ina cikin damuwa magana nake son mu yi, wani abu zan baka" Ya ce "Wani abu me?" "Abu ne mai muhimmanci a kan viper, amma sai ka yi mini alƙawarin ba zaka yi mini faɗa ba ko ka gayawa abba ba" Tattara nutsuwarsa ya yi ya ce "I hope, ba wata kasadar ki ka je ki ka aikata ba" Ta girgiza kai ta ce "Ba wata kasada da na yi, ni dai ka yi ka dawo, kan na mutu" A rikice ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, menene ki gaya mini" "Ka kwantar da hankalinka, kawai dai ka yi ka dawo, abun yana da muhimmanci, na san yadda zaka same shi kai tsaye" "Kin ga ba zan iya jira ba, gaya mini menene sai na aika su Mu'azzam, dama wanda aka kama ɗin nan ya ƙi magana" "Sai ka dawo gaskiya" ta kashe wayar gaba ki ɗaya, dan kar ya biyo ta, ta sake dafe kanta. Sumayya na news room, tana jiran lokaci ya cika, ta gabatar aka turo ƙofar aka shigo. Sak tayi tana kallon mai shigowar. Mutumin da honorable ya saka ya karɓi wayarta ne, ranar da ta je gidansa. Ya ja kujera yana kallonta, ya ce "Ya dai, kin yi mamakin ganina ne? Mintuna goma sha biyar suka rage miki, kan ki fara karanta labaran, zaki yi mini aiki". Ta zuba masa ido, amma ba ta ce uffan ba. "Meyasa ki ke yi mana ƙarya a aikinmu? Da gaske ƙawarki ta haɗu da Viper?" Cikin ɓacin rai Sumayya ta ce "Na gaji da amsa wannan tambayar, idan ba ku yadda da ni ba, ku nemeta ta amsa muku mana" Ya shafi sajensa ya ce "Zamu gani ai, yau ta je court ɗin da aka yi wa Viper shari'a, ta karɓi secret file ɗin sa ta duba, zaki kira ta, ki ji dalilin zuwan ta, da kuma abun da za ta yi da file ɗin" Sumayya ta girgiza kai ta ce "Nabila ba wani abu da za ta amfana muku, kawai na san ƴar rigima ce, so take ta yi suna ta ɗaukaka ta taimakawa yayanta shikenan" Yayi dariya ya ce "Za mu gani, daga yanzu zuwa azahar ɗin gobe, idan baki kawo rahoton dalilin bin diddigin shari'ar Viper da take yi ba, abun da ba kya zato zai faru" ya miƙe tsaye ya ce "lokaci ya cika, ki gabatar da aikinki" Sumayya ta dafe kai cikin matsananciyar damuwa, tana tunanin wannan wace irin rayuwa ce. Murtala ne ya shigo yana faɗin "Afuwan sisyna, mamager ya kira ni ne, na saita komai ki fara". "Ba ka ga mutumin da ya fita yanzu ba?" Ya kalli ƙofar ya ce "Ban ga kowa ba" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan mu fara". *** Ƙaramar wayarta ce isheta da vibration a ƙasan pillow, ta ɗaga ta ce "Bacci fa nake ki ke ta kiran wayata". "Haka dai, daga bacci sai kwalliya da cin abinci, ke har kin koma gida kin kwanta, ni tun 9 gani har 5 ban tashi ba" Nabila ta ce "Ke ba na samun bacci a ƴan kwankin nan wallahi" "Meyasa?" "Wallahi a tsorace nake, ba na iya bacci, gani nake kowane lokaci viper zai kashe ni, cewa yayi fa sai ya kashe ni, sonake Yaya ya dawo na danƙa masa wayar nan, na huta, wai da wayar wa ki ka kira ni ne?" Sumayya ta ce "Wayata ce ta ɗauke, ina ki ka je ne yau?" "Wurin aiki mana, amma da labari sosai, mu haɗu gobe in Allah ya kaimu" "Yakamata mu haɗu kam, dan na ga mutuniyarki bunkure, a gidan honorable Indabo" Daga kan gadon da Nabila take ta miƙe tsaye ta ce "Amma ba ki gaya mini ba sai yau?" "Na san halinki ne, uzzura mini zaki yi, ke bari na tafi gida ma yi magana" Ta kashe wayar, ta kaiwa murtala wayarsa, dan ta fuskanci mutanen honorable na bibiyar kiran wayar da take yi. Wuni guda ramma ba ta sake saka Abdul a idonta ba, sai dai kukunsa idan ya kammala girki, ya ƙwanƙwasa mata ƙofa ya ajiye mata abinci. Tayi kuka har ta gaji, ta koma addu'a, tare da fatan Allah ya kuɓutar da ita daga sharrin zaluncin Abdul. Tana zaune a ƙasan carfet, har wurin sha biyu na dare, ya shigo yana kokawa da ƙofar ɗakin, saboda a buge yake. Ta tashi tsaye cikin tsoro, sai dai ba tare da ta yi masa laifin komai ba, ya hau ta duka, ya din ga ball da ita yana taka ta da ƙafarsa, tun tana kururwa har ta kasa sai ajiyar zuciya, ko ƙwaƙwƙwaran motsi ba ta iya yi. Tamkar dabba haka ya afka mata, ba tare da la'akari da ƙarancin shekarunta ba, kodayeke ina tunani ga wanda hankalinsa ya gushe?. Bai farka ba sai kusan tara na safe, yayi miƙa ya tashi yana kallon ɗakin, da sauri ya kalli gadon bai ganta ba, ya kalli jikinsa, ya tashi yana mayar da kayansa, kawai ya ga jini a gefensa, har zuwa banɗaki, cikin hanzari ya nufi banɗakin, ƙofar tana buɗe dan haka ya shiga, ya tarar da ita a zaune ta jingina da jikin bath jini yana ta zuba daga jikinta, ga jikinta duk a kumbure saboda duka, idonta a rufe. Ya ƙarasa ya durƙusa ya ɗaga hannunta ya saki, ya ga ya koma babu alamar numfashi a tare da ita, rigarsa dake jikinta, tayi sharkaf da jini. Dafe kansa yayi yana tuna abun da ya faru jiya, kamar mafarki. 16 🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143* 16 Shi gashi ko sunanta ma bai sani ba, ya sake ɗaga hannunta, amma hannun ya sake dawowa ƙasa. Ya kai hannunsa hancinta, ya ji tana numfashi kaɗan-kaɗan. Ya haɗa ruwa a bath ɗin mai ɗumi, ya cire rigar jikinta ya ajiye a gefe. Ya ƙarewa jikinta kallo, ko ina shatin duka ne da ya yi mata, take wani abu mai kama da tausayinta ya ɗarsu a ransa, ya ɗaga ta, ya sakata a cikin bath ɗin, ga abun da ta yi ɓari nan daga cikinta a ƙarƙashin ta. Duk da ƙyanƙyaminsa, da yadda ƙarnin jinin yake hawar masa ka, haka ya din ga tarar ruwa, yana kwarawa a banɗakin, ita kuma ya din ga canza ruwan da take ciki, saboda yadda yake ɓaci da jini. Rigarta kuwa, wuri guda ya ware ta, dan kuwa yarwa zai yi, bai san yadda zai yi da ita ba. Ya fita da sauri, ya kira mai aikinsa solomon, ya rubuta masa abubuwan da yake buƙata ya ce ya sayo masa. Har solomon ya je ya dawo, yana ta ƙoƙarin ganin ya tsayar da jinin da take zubarwa. Ya ɗauke ta zuwa kan gado ya kwantar da ita kamar gawa, ya sake ɗiban jininta, ya yi bawa solomon ya ce ya kai kowane lap ne, idan ya kai ya kira shi a waya. Ya saka mata drip hannu biyu, ya sake su, yana yi yana duba vitals ɗin ta. Ƙofar ɗakin ake ta bubbugawa, ya tashi ya buɗe, ya ga saif a tsaye. Saif ya kalleshi ya ce "Ya na ganka kamar mara gaskiya? Lafiya kuwa?" Ya girgiza kai ya ce "Ina fa lafiya, yarinyar nan ce tayi miscarriage" Saif ya ce "Shi ne me to? Dama ba haka kake so ba, na ga ma fa kasheta za ka yi ka bar ta" Abdul ya ce "Haka ne, jiya daka sauke ni bayan ka tafi, ka san a buge nake, na dake ta sosai" "Lallai Abdul, yau ka fara yi wa mata haka to?" Ya girgiza kai ya ce "No, kawai su sauran su ne suke kawo mini kansu, shiyasa ban taɓa jin komai ba a kan abun da nake aikatawa, sai ta ji sauƙi sosai, zan kasheta na huta" Saif ya ce "Well mu je in ga jikin nata" Abdul ya tsaya a gaban ƙofar ya ce "No, ba zaka shiga ba" Cikin mamaki ya kalli Abdul ya ce "Lafiyarka kuwa?" "Ras nake, ba zaka shiga bane kawai" "Ka kashetan kenan?" "Idan na kasheta, zan kasa gaya maka ne, ko tsoronka nake ji?" Suna haka solomon ya kira shi, ya haɗa su da masu lap, ya gaya musu gwaje-gwajen da yake so a yi wa jinin ramma da ya bayar aka kai. Ya koma ɗakin da take, ya rufe ya saka mumulli, ta ciki, ya sake nufar gadon, ya hau yana tattaɓata ya ga ko ta na da rai. Ambaton Allah ya ji tana yi, tare da kiran sunan mama ƙasa-ƙasa, sai dai bai ma san sunanta ba balle ya kira sunan. A hankali ta buɗe idonta a kansa, ta yinƙura za ta tashi, amma ta kasa, duk jikinta ciwo yake yi, mararta ma wani irin ciwo take yi mata. Ya riƙe hannunta, yana tsareta da idanunsa ya ce "Sannu" Hawaye ya shiga ziraro mata ta gefen idonta ta ce "Me na yi maka jiya ka dake ni?" Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "A buge nake ne ba abun da ki ka yi mini" Cikin ƙarfin hali ta ce "Allah ya saka mini, na barka da Allah" Ya amsa da "Tom" Ta sake yinƙurawa za ta tashi, amma ya riƙeta ya ce "Ina zaki?" "Salla zan yi" Abdul ya ce "Ki na zubar da jinin zaki yi salla?" Ta  ɗan gyara kwanciyar ta, cike da takaicin yanayin da take ciki, da kuma kallon da yake yi mata, cikin marairaicewa ta ce "Dan Allah ka rufe mini jikina, ka daina kallona". Da idanunsa ya tsatstsareta, yana yi mata wani irin kallo, da ya ƙara ɓata mata rai, ta ɗaga hannunta da kyar, za ta ja zanin gado da ya rufe mata ƙafa, ta rufe jikinta da ko arzikin vest babu, amma ya riƙe hannunta, ya mayar ya ajiye wuri guda. Ya ce "Idan ruwan nan ya goce, mutuwa zaki yi, dan kin zubar da jini sosai, kuma bana fatan ki mutu yanzu, sai kin samu ciki, kin haifa mini ɗa, saboda zuciyata ta so abun da yake cikinki, ya zube". A hankali ta cigaba da sheshsheƙar kuka, tare da fatan ta mutu ta huta da wannan bayahudiyar rayuwar da ta faɗa, duk a silar talauci da rashin galihu, ta san Allah kaɗai ya san halin da mahaifiyar ta take ciki, na tashin hankalin rashin sanin in da take. Idonsa ya sauka a kan taruwar jinin da ya kwanta a gefen wuyanta, ya ƙara tabattar da ba ƙaramin duka ya yi mata ba. A karo na farko da ya ji waji abu mai kama da tausayin wani ya shiga ransa, she look very innocent and calm. *** Tun da Nabila ta shiga office ɗin Barrister Habib, take murmushi, shi ma murmushin ya yi mata ya ce "Ya ake ciki ke ƴar ƙwalisa" Ta zauna tare da faɗin "Godiya nake barrister, jiya ai na je, an bani duk abun da na buƙata, na gode sosai da sosai Allah ya saka da alkhairi" Barrister Habib ya amsa da "Amin ya rabb, ina fatan babu wani abun?" Ta ce "Akwai, abubuwan da na gani sun ɗaure mini kai, ashe kisan kai yayi" "Ba abun mamaki bane ba, dan mutum irin wannan ya yi kisan kai ai". Ta ce "Haka ne, amma shekara biyar ya yi ba a yi masa shari'a, kuma aka sake shi, ba tare da wani cikakken dalili ba, gaba ɗaya ma akwai abubuwan da babu a cikin file ɗin nasa ma" Ya ce "Nabila cases irin wannan ai da yawa, sai fatan Allah ya kyauta" Ta amsa da "Amin, yanzu saura alƙalin da ya yi masa shari'a, na ga an rubuta justice zakariyya, amma babu surname ɗin sa" Barrister Habib ya yi murmushi ya ce "Shi kuma me zaki yi masa?" "Kawai so nake na sani" "Ai an yi masa transfer ma daga kano, bama ya ƙasar ya je ƙaro karatu" Nabila ta ce "Kuma duk hakan yana da alaƙa da case ɗin viper?" "A'a ba na ce ba, na dai san shi ne before, bani da tabbacin yanzu" Ta ce "Na fahimta, na gode sosai da sosai, bari na je zan ga Sumayya, yanzu zan dawo, na yi mata alƙawarin haɗuwa da ita yau" Ya ce "Ok, Allah ya tsare" Ta tashi ta fita, dan kuwa yau ba ta da aiki sosai. Sosai take son ganin sumayya, domin ta ba ta labarin halin da ake ciki, a kan binciken da take yi a kan viper. Ta kira sumayya ta ce mata za ta shiga gidan radiyonsu, su haɗu a can. Tana fitowa daga gate ɗin, ta tarar da wani mai napep a tsaye, ta ce "Malam tafiya zaka yi?" Ya ce mata "Eh" "Yauwwa, mu je" ta kama adaidaita sahun ta shiga, tana ƙoƙarin ɗaga kiran da yake shigowa wayarta. Sai dai ba ta kai ga hakan ba, wasu matasa suka shigo napep ɗin, suka zauna a gefe da gefenta, suka rufe mata baki da ido, mai adaidaita sahun ya ɗauke kan babbar hanya ya yi wani wurin. Kusan awanni biyar, ramma ta ɗan samu ƙwarin jikinta, har ta samu ta yi wanka, sai dai ta kasa cin komai, ya sake ba ta wasu kayan a cikin nasa, duk da sun yi mata yawa, ta karɓa ta saka, ya ja hannunta zuwa falo. Solomon ya kawo abinci, da fruit, Abdul ya kalleta ya ce "Me zaki ci a nan?" Ta girgiza kai alamar a'a. "Wallahi ko ki ci abinci, ko na sake yi miki tsinannnen duka a wurin nan, bana son shashanci bar ganin ina lallaɓa ki" Cikin tsoro ta din ga cakalar abincin, tana ci tana kuka. "Ke, meye sunanki ne ma?" Jiki a sanyaye ta ce "Ramma" Ya yatsine fuska ya ce "Meye wani ramma, ba rahama ba?" "Eh rahama"ta amsa tana sunkuyar da kai. "Meye yake yi miki ciwo yanzu?" Ta ja majinar da take shirin zubo mata, ta goge hawayenta ta ce "Duka jikina" "Dukan da na yi miki ne, gama mu koma ɗaki, sai na yi miki tausa" Manyan idanunta ta kafa masa, tana kallonsa. "Ki daina kallona da wannan ƙwala-ƙwalan idanun naki, idan ba haka ba, na fita sai kin ganni". Ta din ga wasa da doyar, ta kasa ci, ta kuma rasa abun yi. Shiru-shiru sumayya ta din ga kiran wayar Nabila, ga wayar na shiga, amma ta ƙi ɗagawa har ranta ya fara ɓaci, gefe guda kuma ga mutanen honorable na ta kiranta su ji, yaya suka yi me Nabila ta yi da file ɗin viper da ta je nema. Nabila ta na ji aka sauko da ita daga cikin adaidaita sahun, bayan shafe lokaci ana tafiya. Babu bakin magana, an rufe mata baki, an ɗaure mata ido, sai addu'a kawai take yi a zuciyarta. Kwance mata idanu suka yi, ta yi tozali da Walid a gabanta yana yi mata wani irin mugun kallo, sai da hantar cikinta ta kaɗa. Wurin da suke kamar jeji, babu gida gaba babu a baya, sai shi da ƴan daban da suka kawota, ashe mai napep ɗin nan ma duk set up ne. Jikinta ya hau tsuma, sai dai ta kasa magana, amma duk da haka godewa Allah take yi, da ba wurin Viper suka kaita ba. "Yanzu abun da ki ka yi kin kyauta kenan?" Walid ya yi maganar yana tsareta da idanunsa. Ta sunkuyar da kai, ya daka mata tsawa ya ce "Tambayar ki nake yi, da ki ka saka a ka kama liti shi laifin me yayi miki, ina har in da Vipern yake kin sani, kuma kin je, meya hana ki tura kai tsaye a kama shi? Yanzu gashi ina ta fama da shi, ya ce lallai zai miƙa kansa ga hukuma, saboda a saki liti, ba zai sake bari wani ya wahala saboda laifinsa ba" Cikin dakiya Nabila ta ce "Dama haka ne ya dace da shi ai, mutumin da yayi kisan kai aka sake shi, kuma yake zubar da jinin mutane ai hakan yakamata yayi, ta haka ne zai wanke nauyin laifukan da ya aikata" Walid ya ce "Haka ki ka ce? Da ya yi kisan kai wa ya kashe?" Ɗaya daga cikin su ya ce "Me gida, ka bari mu cire mata ta yatsu ko za ta dawo hayyacinta, ji fa maganganun da take faɗa a kan master". Ya ɗaga musu hannu, ya dube ta ya ce "Shikenan, kin yi gaskiya yayi kisan kai, zan bar Al'amin ya miƙa kansa ga hukuma, amma ki sani duk hukuncin da aka yi masa, ke zaki ɗauki nauyin alhakinsa, idan ma amfani ake da ke dan cimma wata manufa a kansa, wanda suke amfanin da ke sun bar ki a duhu, amma kafin nan yakamata ki san waye Al'amin, meyafaru da shi, daga nan kuma duk abun da ki ka yanke ya rage naki!!!. GUNDARIN LABARIN. Tsaki yake tayi a jejjere, yana kaiwa yana komowa a matsakaicin falon, yana sauke numfashi. Matar da ke zaune a kan kujera ta kalleshi ta ce "Wai yanzu dan Allah wannan sintirin ne zai baka mafita?" Kamar mai jiran ƙiris ya ce "To yaya zan yi? Magana fa ake ta makomar siyasata, idan muka faɗi zaɓen nan akwai matsala, kuma malamin nan ya tabattar mini da na cika kowane sharaɗi, sai zubar da jini ranar zaɓe, kuma alamu sun nuna gwamnati da gaske take, za a tsaurara tsaro sosai da sosai a wurin zaɓen nan, kuma idan ba a cika wannan sharaɗin ba, komai fa ya rushe" Matar ta numfasa ta ce "Duk ina yaranka marasa jin nan ne, da suke yi maka aiki?" "Bilki duk suna hannu, kuma babu wani cikakken jan wuya da zai iya tarar aradu da kan nan, idan aka kama mutum da tayar da tarzoma a wurin, shekara sha biyar ne a gidan yari". "To sai me, kai zaka yi, ka biya su su yi aiki kawai". "To ai ki gane, duk sun tsorata da hukuncin ne" Bilki tayi murmushi ta ce "Ka fito da mai dogon zamani mana, kai ka san zai iya, Al'amin ba" Ya kalleta sannan ya nemi wuri ya zauna ya ce "Kuma fa kin kawo shawara, sai dai yaron ne hukuma ne sai da rarrash, ban taɓa ganin ɗan iska mai mulkin tsiya ba sai shi, tsaf zai ƙi yi, saboda kusan watanni shida yana tsare ban fito da shi ba" Ta ce "Amma ai yana jin maganar ka, zai yi ba ni da wata tantama" Ya jinjina kai ya ce "Hakan za ayi, zan saka a fito da shi" *** Sanye take da dogon hijjabi launin maroon, har ƙafarta hijjabin ya ɗauki guga, ƙafarta sanye da safa baƙa, sai sauri take yi tana ratsa lunguna har ta iso ƙofar gate ɗin makarantar islamiyyar. Sai dai duk wannan saurin da take yi, an riga an fara tarar makara, wanda idan da abun da ta tsana, shi ne a taɓa lafiyar jikinta. Kusan mintuna goma ya ƙara, bai shiga ajin ba domin yi musu ƙari, yana jira ya ga ta ina za ta ɓullo, yana ofishin malamai, yake hango yadda malam hamza ya zage ƙarfin sa, yana shimfiɗa mata murtukekiyar dorina a jikinta, sai kuka take tana bashi haƙuri. Sam bai ga fa'idar duka a cikin ladabtar da ɗalibai ba, mussaman mata, macen ma mai rauni kamar wannan baiwar Allah. Litattafan sa ya kwasa, ya tafi ajin nasu, malam Jamil kenan, ba ya duka ba ya zagi da cin mutuncin ɗalibi, amma ɗalibai na ganin girmansa da mutuntashi. Ana tsaka da tilawa ta shigo ajin, ta nemi wuri ta rakuɓe a gefe, ɗaya bayan ɗaya ɗaliban suke tasowa, suna zuwa gabansa da littafi, suna bayar da haddar Alqur'ani mai girma, idan ya kammala ji, ya rubuta maka making haddarka, sauran ɗalibai kuma na cigaba da tilawa, sai dai fiye da rabin hankalinsa yana kanta. A haka har aka zo kanta, ta tashi jiki babu ƙwari, ta je gabansa ta zauna, ta miƙa masa littafinta, ya karɓa yana dubawa, ba bu in da take da maki ƙasa da casa'in da biyar. Tayi bisimillah, ta fara karanto wurin haddarta, sai dai ba aje ko ina ba, muryarta ta fara rawa, kuka ya ƙwace mata, bai ce mata uffan ba, ya cigaba da kallon ɗaliban, tamkar haddarta yake ji. Sai da tayi sosai, sannan ta cigaba da karatun, tana yi tana share hawaye. "Ba kya son duka meyasa ki ka makara?" Maimakon ta bashi amsa, sai ta sake fashewa da kuka. "Kin ci abinci ne?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "Wani abun suka yi miki a gidan" ta girgiza kai alamar a'a. "To ni wannan haddar taki, ban ji ta sosai ba, dan haka sai kin sake wata, je ki zauna, kuma ki daina wannan kukan" ta jinjina masa kai, ta share hawayenta. Sai dai zamanta ke da wuya, sai ga malam hamza ya shigo da dogon littafi, yana muzurai. Yayi wa malam Jamil magana sannan ya ce "Duk wanda ya ji sunansa, ya tashi ya je gida, kar ya sake zuwa sai ya biya kuɗin term, tun da ba da yawun bakinmu zamu biya malamai ba, tun da iyayenku ba sanin darajar malaman addini suka yi ba, da dai na boko ne. Sunan farko sunanta ya fara kira, ya ce "Ke waliyiyya, duk term sai an kore ki, sai an yi ta artabu kan ki biya kuɗin term, duk wannan uban shirgegen gidan naku, dubu uku a wata uku sai an yi ta fama, tafi gida idan kin karɓo kuɗin kya dawo". Ba wannan ne karon farko da aka koreta saboda kuɗin makaranta ba, sai dai a duk lokacin da aka koretan, ta kan ji ta muzanta ainun. Haka nan ta ɗauki jakarta ta tafi gida, tana zuwa gidan ta tarar da wata babbar mace ta shirya za ta fita unguwa, ita da wata budurwa. "Me kuma ki ka dawo yi, an tashi ne?" "A'a mama, wai kuɗin makaranta aka turo ni na karɓa" Matar ta kwaɓe baki ta ce "Uban naki bayanan ai, tun da kin dawo dama unguwa zan je, maza ki ɗora girkin dare, bana son yin daren girkin nan" ta amsa da to. Budurwar ta ce "Yauwwa Jauhar, akwai kayana a kan gado, dama jibi zan koma school, tun safe nake jiran mai wanki, ya zo ashe ya tafi gida, kya wanke mini, har bedsheets ɗi na, bargona kuma na jiƙa shi, yana baya, idan ya so kan mu dawo idan sun bushe, ko gugar kya rage mini ki goge su". Ta sake amsawa da "To, sai kun dawo" Ta ƙarasa ɗakin da take kwana, ta hau cire uniform, ranta babu daɗi, duk ƴan gidan suna makarantun islamiyyar su, ita kuwa an korota daga ta su, kullum sai an kai ruwa rana kan a biya mata kuɗin makaranta, alhalin sauran har na term uku ana biya musu. Ta canza kayanta zuwa na gida, ta shiga kitchen ta kunna gas, ta tarar ya ƙare, ba ta jira komai ba ta ɗebi itace, ta fita garejin gidan, ta tayar da wuta ta ɗora girki. Ba ta fi shekara goma sha shida ba, amma yadda take sarrafa jikinta tana aiki, kamar wata babba. Tana girki tana wanki, a haka ƴan islamiyya suka dawo, kowa ya watsar da jakarsa, da uniform ɗin sa, masu ball suka tafi, masu wasa suka fita, duk suka sake ɓata gidan, ta bi ta sake tattarewa, ta haɗo kan kayan da suka watsar su ma ta zuba ruwa za ta wanke. *** Fuskarsa murtuk, kamar bai taɓa dariya ba, haka ya tunkari ƙofar gidan, yana wata irin tafiya, mai kama da ta ƙasaita, maimakon ya saka hannu ya buɗe ƙofar gidan, wani irin duka ya yi mata da ƙafarsa, ya shiga ba tare da ko sallama ba. "Wane mara hankalin ne yake dukar mana ƙofa haka, sai ya karya..... Shiru ta yi ta haɗiye sauran maganar, ganin wanda yake tsaye ƙerere a gabanta. "Yaushe ka fito? Ko in ce waye ya fito da kai?" Ko kallonta bai yi ba, ya cigaba da takun ƙasaita, ya je ya tura ƙofar wani ɗaki, ya shiga sai dai babu kowa a ciki, dan haka ya fito ya nufi kitchen. "Al'amin kar ka shigar mini kitchen, ban dafa komai da kai ba, na ga lokacin fitowarka daga prison ma bai yi ba, wannan jaraba da masifa Allah ya yi mini maganinka" ba ta gama maganar ba, ya fito daga kitchen ɗin, da kulolin abinci. Shan gabansa tayi ta ce "Kar ka taɓa mini abinci, abincin ƴaƴana ne da na mijina, bana son tashin hankali Aminu, ka je ka ajiye mini" Take ya juya idanunsa yayi mata wani irin kallo, a take ta ja da baya ta koma gefe, tana bin fulasan hannunsa da kallo. Wani irin fito ya yi, wani daga waje ya amsa masa da fiton, ya fita da fulasan abincin ba tare da ya amsa ko ɗaya daga maganganun da matar ke ta yi masa ba. Jauhar kuwa, kafin magariba ta kammala girkin nan, ta kawwame a flask, sai gyara gidan take yaran suna ɓatawa, da masu hankalik cikinsu da marasa hankalin duk babu mai taimakawa a gyara. Ta ɗauki abincin maigidan ta kai masa ɗakinsa. Tana idar da sallar magariba, ta shirya ta ɗauki jakarta, dan tafiya makarantar dare. Tana fita maigidan yana dawowa, yayi parking ya sauke glashin motar ya ce "Waliyiyya an fito?" Murmushi ta yi, sai da fararen haƙoranta suka bayyana ta ce  "Baba kai ma waliyiyyar zaka ce mini?" "Eh mana, ba haka malamanku suke ce miki ba, za a tafi makarantar ne?" Ji tayi kamar tayi masa maganar kuɗin term ɗin ta na islamiyya, amma ta kasa, mussaman da tuna gargaɗin mama da tayi mata. Ta ce "Eh baba, sannu da zuwa, na kai maka abincinka ɗaki ma, kana zuwa sai dai ka ci" Yayi murmushi ya ce "To Allah ya yi albarka, a kula sosai ayi karatu da kyau" Ta ce "In sha Allah" ta wuce makaranta shi kuma ya gyara parking. Gudun kar ta makara a makarantar dare, ya sanya ta fita ba ta ci abinci ba, duk da yunwar da take ji, ta ce idan ta dawo sai ta ci. Sai dai bayan dawowartata, ta tarar da an cinye komai. Cikin girmamawa ta ce "Mama an cinye abinci ne?" Mama ta kalleta ta ce "Au ba ki ci ba dama?". "Eh, na rana ma ban samu ba, na rufe nawa saboda kar na makara na tafi makarantar dare". "Eh to ai yayi kyau, al huda huda ina da littafi, to an cinye ki zuba ki ci kan ki tafi ba zaki iya ba, duk salon ace zaluntarki ake yi ba a baki abinci, kin wa kanki ai, ni ki hanzarta ki yi wa yara gugar uniform, tun da ga wuta, kar a ɗauke" Ran jauhar ya sosu rashin samun abincin nan, dan har ga Allah tana jin yunwa sosai da sosai, sai dai babu yadda ta iya, dole ta shiga ta kwaso tulin guga ta hau yi. Tana gugar nan zabga-zabgan ƴan matan gidan suna kawo mata karon nasu, har wurin sha biyu na dare tana abu ɗaya, ga cikinta sai ƙara yake yi tana hamma, ga bacci da gajiya, ga kuma yunwa. Bayan ta kammala guga, ta bi manyan ɗakunansu ta ba su, ta kai na sauran yaran ɗakin iyayensu, sannan ta koma ɗakinta, ta yi alwala tayi sallar isha'i, ta yi shafa'i da wuturi, ta nemi ta kwanta. Ba ta yi mintuna goma sha biyu da kwanciyar ba, ta jiyo ana ƙwala mata kira a tsakar gida. Haka ta sake yinƙurawa, ta fito matashin saurayi ne, tsaye hannunsa riƙe da leda ya kalleta ya ce "Kin fara bacci ne?" Ta ce "A'a yaya, idona biyu" "To ga indomie nan, faka-faka dafa mini dahuwar nan taki, mai muslmin daɗi, akwai gasashshiyar hanta a ciki da ƙwai, na san akwai attaruhu da alabasa a gidan, tayi yaji fa sosai" Ta karɓa ta ce "amma yaya da daddare nan ka ci yaji ka kwanta, ulcer fa" Zare mata ido yayi ya ce "Sai kin saka an yi mini faɗa ko, maza dafota ƙwan nan fa ya soyu shi ma" Tayi murmushi ta koma ta sake gangamin haɗa wutar da ƙanan itace, dan kuwa, ta riga ta kashe murhun, kuma ba ayi refilling ba. Kasancewar a gareji take girkin, sauro yayi mata rubdugu da cizo, sai da wutar ta kama sosai, hayaƙi ya kore su. Sai da ta gama tana juye masa, sai gashi ya shigo, hannunsa da leda ɗauke da lemon roba mai sanyin gaske. "Yauwwa waliyiyya, Allah dai ya tuttula miki albarka, ya baki miji nagari" ta sunkuyar da kai cikin jin kunya. Ya samu wuri ya zauna, ya ce "Samo plate ki ɗiba, sai ki jiye mini sauran" "A'a ni fa a ƙoshe nake, ka bari na lashe tukunya, ka san ina son romon indomie" Yayi murmushi ya ce "Ke ce romon ai" Ya zuba mata a tukunyar, ya datsar mata ƙwan, jikinta har tsuma yake yi, tana hannu baka hannu ƙwarya, ba tare da ta san tana hakan ba. Yadda ya lura tana ta suɗar kwanon, ya san babu lallai ta ci abinci yau, dan haka ya sake tura mata ta gabansa ya ce "Ungo na ƙoshi" Ta ɗan yi saroro ta ce "Yaya Saifu ba daɗi ne?" "Ina fa, ke kin san duk duniya, babu wanda ya kai ki iya dahuwar indomie, ƙoshi nayi kawai, ki hanzarta ki gama ki je ki kwanta, dare yayi" Ta karɓa ta yi masa godiya. Sai dai tana gama ci, wani matashin da zai girmewa saifu ya fito, ya zube mata kayansa na ƙwallon ƙafa, har da takalmi, sai tsamin rana da warin hammata suke yi, ya ce ta wanke masa kafin ta kwanta. Kamar saifu yayi magana, amma yayi shiru ya fasa. Ƙarshe ba ta kwanta ba, sai ɗaya da rabi na dare, shi ma ko da ta tuna, kwanaki kaɗan suka rage mata jinin al'ada ya zo mata, gashi ba ta da audugar tare jini, ga kuma kuɗin makarantar islamiyyarta, babu shiri ta fasa kwanciyar, ta ɗaukko kwanon da take zuba dutsen da take shiri da shi, ana biyanta, tana tara ƴan kuɗi, duk da shirin ba wata riba ce da shi ba, amma yana taimaka mata sosai. Tamkar mai shirin hawan aljanu, haka ta haƙiƙance, tana zuba masa bala'i, "Wallahi ba zai yiwu ba, dole ka zaɓa ko ni ko ɗan ka, idan har zai cigaba da shigowa gidan nan, to wallahi ni zan bar shi, dan ba zai illatani da yarana a banza ba, ko ya lalata mini ƴaƴa ba. Sanin kanka ɓaras ya karya mini ɗa, Allah ne yayi da sauran rabon Musa ya taka ƙafarsa a duniya, ga ni da yara mata, ya din ga shiga yana fita, ba ma wannan ba, yadda ya yi ƙaurin sunan nan a duniya, tsaf zai hana mini  ƴaƴa auruwa, to wa ma zai zo ƙofar gidan nan zance, yana tsoron a raba shi da rayuwarsa, ba zai yiwu ba gaskiya". Ya numfasa ya ce "Rahila, da wani idon ki ke so duniya ta kalle ni? Idan na kore shi na hana shi zuwa gidan nan, yana da in da ya fi nan ne?" "Idan ba shi da shi ka nema masa, ni fa ba zan cigaba da rayuwa da tantirin ɗan daba a cikin gida ba, ya sabauta mini rayuwata da ƴaƴana ba, Allah ya mayar da shi kurku ya dauwwama a can kowa ya huta, ina dalili za a hana ni rawar gaban hantsi, mutum ba tarbiyya duk na sangarta shi, an mutu an bar mutane da masifa da bala'i a bayan ƙasa, me ake da ɗa irin wanda zahra'au ta mutu ta bari, Aminu ai cikon asara ne a cikin al'umma, wallahi ta yi asarar haihuwa". Yana tsaye a bakin ƙofar shiga falon, yadda ta ɗaga murya, ya sanya ya ji komai, zuciyarsa ta din ga wani irin hanƙoro, wani abu mai masifar ɗaci ya din ga taso masa. Ya saka hannu ya danƙe handle ɗin ƙofar iya ƙarfin sa, saboda muddin ya shiga cikin falon, yadda yake jin sa a saman nan, ya cake da wiwi, babu abun da zai hana shi ɗaga matar nan, ya buga da ƙasa. Ya kasa gaba ya kasa baya, shi bai shiga ba, kuma bai bar wurin ba, kunnuwansa suka cigbaa da karɓar miyagun maganganun da take faɗa a kansa. Ƙarar da handle ɗin ya bayar ne, ya sanya su juyowa su kalli bakin ƙofar, ɓaras ya karya handle ɗin nan, duk ƙwarin sa, ya fara yi mata wani irin kallo, da ta kasa gane ma'anarsa. Ayshercool 08081012143 17 🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143* Da sauri ta ɓuya a bayan maigidan, hantar cikinta na wani irin kaɗawa. Ya nuna kansa da yatsansa ya ce "Haihuwata ce asara ko? Ni?" Cikin tsawa ya ce "Kai aminu, ya isheka haka, kar ka kuskura ka aikata wani rashin mutunci, ko ka ce zaka yi mata wani abu, koma menene ba kai ka janyo ba, ka nustu ka zama mutumin kirki mana, kalli yadda ka yi shuhura a shashanci da harkar sara suka, ni kaina ban so fitowarka ba wallahi, yanzu zaka zo ka cigaba da ɗaga mini hankali, ka hana ni zaman lafiya da iyalina, dan haka ka bar mini gida, kar ka sake shigo mini gida, ba na buƙatar ka". A hankali ya saki handle ɗin ƙofar da ya karya, ya kalli mahaifinsa ya ce "In daina zuwar maka gida, Abbu ina zani? Wurin wa zan je?" "Ka je duk in da ya yi maka, ko wurin ƴan iskan da suka ka ke jin maganar su sama da tawa, amma kar na sake ganinka a gidana" Yayi murmushi mai ciwo, ya ce "Shikenan, zan tafi zuwa lokacin da huce zan dawo" "Ba na buƙatar dawowarka, tun da ban isa da kai ba, ka je ka ƙarata" Tuni idanunsa suka rine, zuwa launin ja jawur "Ba a canza tuwo suna, ba ni da wanda ya kai ka ko ya fika, ba ni da gidan da yafi nan, dan haka ba zan daina zuwa gidan nan ba, amma idan ka matsa zan tafi, idan kuma na tafi na bar shi kenan har abada, wani aiki aka fito da ni na yi, da yiwuwar idan na gama aikin, na koma gidan yari, komawar da ba zan sake fitowa ba, sai ku huta da ganina" ya ƙarasa maganar kafofin gashinsa na mimmiƙewa saboda ɓacin rai. Rahila ta ce "Allah ya raka taki gona" Juyawa ya yi ya fice, har da sassarfa, dan yanzu abun da zuciyar sa ke raya masa, ba iya ya bugata da ƙasa bane, ya raba maƙogwaronta da wuƙar ƙugunsa haka yake ji. Tafiya kawai yake yi, yana tunani barkatai a cikin zuciyarsa, har ya ƙarasa in da yake son zuwa. Suna ganinsa suka mimmiƙe tsaye, sun risunar da kawunansu, tamkar dai yadda ake yi wa shugabbani, a wurin shugabancinsu, ba tare da ya ce komai ba ya zauna, yayi shiru. Liti ne yayi gyaran murya ya ce "Allah ya taimaki mai dogon zamani, menene damuwarka ne?" Al'amin yayi shiru, dan shi bai san me zai ce ba ma. Ba yadda ba su yi da shi ba, amma yaƙi magana. Liti ya miƙo masa wani satchet ɗin magani, ya ce "Ga wannan ka sha rabi, yanzu za ka ji ka ɓata, ka manta komai, wasu ƴaƴan matsalarka duk za su sauka, daga hau ka saukko za ka ji komai ya goge" Ya saka hannu ya karɓa, yana jujjuya satchet ɗin. "Ka saka ɗaya a ƙasan harshenka, shikenan". Ya ɓalli ɗayan ya saka a ƙasan harshen sa, ya jingina da bango, zuciyarsa na cigaba da tafasa. Sai dai bai fi mintuna sha biyar ba, idanunsa suka fara lumshewa. Yayi gyaran murya ya ce "Liti" Liti ya ce "Boss". "Chairman ya fito da ni saboda na yi masa aiki, ya ce na je yana son ganina, zai gaya mini aikin da zan yi masa, sai dai kafin na yi masa aikin zan yi nawa, ko da kuwa zan koma gidan yari ban yi nasa ba" "Allah ya taimaki maza, wane aikin ne, a shirye muke mu yi maka ko menene" Ya jinjina kai ya ce "Madaki zan kashe! Sai na kashe madaki!!" Liti yayi turus ya ce "Maza, duk lokacin da muka yi yinƙurin ɗaukar fansar nan, wahala muke sha madaki fa har tsafi yake yi wallahi, ya gagaremu" Ya ɗora yatsansa a kan laɓɓansa ya ce "Shhhh, ni bai gagare ni ba, zan kashe shi na koma gidan yari" Liti ya ƙura masa ido sannan ya ce "Maza ko ƙwayar ta fara yi maka aiki ne?" Ya buɗe idanunsa da suka yi ja, ya kalli liti, sannan ya mayar ya lumshe su a hankali, bacci yayi awon gaba da shi. *** Rana ta take sosai, ƴan makaranta na ta ɓullowa da ga lungunaa da titunan unguwannin. Sosai jauhar take sauri, ta je gidan da take yi musu shirin dutse, ta kai wanda ta yi, ta karɓo wani su bata ƴan kuɗaɗenta. Babban layi ne sosai, ababen hawa na kaiwa suna komowa, ta tabattar babu abun hawa, wata danƙareriyar mota, ta shawo kwana a guje, ba tare da ko yin horn ba. Gaba ɗaya ta ruɗe, ta kasa gaba ta kasa baya, kawai ta tsaya ta ɗora hannunta a kan ta, tana maimaita lahaula wala ƙuwwata illa billah. Da ƙyar ya iya cin burki, ya fito a fusace mutumin, babban mutum ne sosai, ya kusa sa'an Baba ma, ya hau ta da faɗa "Ba kya gani ne, wannan wani irin rashin hankali ne?" Ta kalleshi da fararen idanunta ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri, wallahi na duba ban ga mota ba, ka yi haƙuri dan Allah" Mutanen wurin da suka saddaƙar sai ya buge Jauhar, suka taso suna salallami, sai dai aka rasa me nuna masa shi ne yayi kuskure, saboda uwar shaddar da ta bi lafiyar jikinsa ta kwanta. Sai kuma jikinsa yayi sanyi, ganin yadda take ta bashi haƙuri, duk da shi ne mara gaskiya, pressure da yake ciki da tension ne ya sanya shi hucewa a kanta. Sai kuma ya kwantar da murya ya ce "Ki yi haƙuri, ai ba ki ji ciwo ba ko?" Ta ce "Babu abun da ya same ni" daga haka ta tsallaka ta shiga layin da take son shiga. Kusan dozen biyar tayi na shirin, aka bata naira ɗari da hamsin, ta kuma karɓo wani tana lissafin saura ɗari biyu da hamsin, ta samu kuɗin pad, wanda magana ake ta saura ƴan kwanaki jinin ya zo. *** Al'amin ne zaune a kan kujera, yana wasa da zoben azurfar hannunsa, Indabo yana ta bayani, amma sam hankalinsa ba a kansa yake ba, dan bai san me ma yake faɗa ba. "Aminu magana nake fa" Ya ɗaga idonsa ya kalle shi ya ce "Ina jinka" "Yaƙin neman zaɓe da zan je, ina son a zubar da jini ne, a tayar da tarzoma ayi hatsaniya sosai da sosai, sai kuma ranar zaɓe" Ba tare da ya kalle shi ba ya ce "Shiyasa ka fito da ni, saboda zan yi maka aiki shi ne ka fito da ni ko?" "Eh saboda haka ne, kai ne ba ka ji, ka fiye rigima, na yi na yi ka fita sabgar madakin nan, ka haƙura, amma kamar annabi da kafiri, kullum cikin harin juna ku ke, kai ne faɗa a nan kai ne a can, wai fa har sayen rigima ka ke yi" Ya katse shi da cewa "Nawa zaka biyani?" "Zan baka dubu hamsin kai da yaranka". "Ɗaurin shekara biyar a gidan yari, shi zan yi a dubu hamsin ni da yarana, ka duba babbar kasada ce" Indabo ya yi murmushi ya ce "Baka da matsala in dai kuɗi ne" Ya tashi tsaye ya ce "Kamar yadda ka yi a wannan karon, ka neme ni kai tsaye, haka nake son ya cigaba da kasancewa, ba na buƙatar sanya wani P.A ɗinka ya neme ni, ya sanar mini da saƙonka" "Na fahimta, ka san mu ƴan siyasa dole sai muna yi, muna ɓad da sahu, baka da matsala". Al'amin ya jinjina kai, ya sa kai ya bar falon, cikin takun ƙasaita. ***** Saifu ne ya shigo gida, wajen ƙarfe uku da rabi, ya tarar da Jauhar tana wanki a tsakar gida, gidan babu kowa, yaran duk sun tafi makaranta. Ta ɗago ta ce "Yaya sannu da zuwa" Ya amsa da Yauwwa "Ina makarantar islamiyyar?" Shiru ta yi ta sunkuyar da kai, ba ta amsa masa ba. "Da ne nake fa" "Amm..dama ban biya kuɗin makaranta bane, sun ce kar na sake zuwa sai na biya" "Kuna kin gaya wa Baba?" Ta girgiza kai alamar a'a. Cikin takaici ya ce "To saboda me?" Ta yi shiru ba ta ce komai ba. Saifu ya ce "Ke dai sokuwa ce wasu lokutan, dubu uku ne ko? Tashi ki saka uniform ki tafi" yayi maganar yana ciro kuɗi daga aljihunsa, ya miƙa mata dubu uku. Fuskarta ta faɗaɗa da murmushi, ta saka gwiwoyinta a ƙasa, ta saka hannu biyu ta karɓa ta ce "Na gode sosai da sosai yaya, Allah ya ƙara arziki". Ya ce "Amin, bar wankin, tashi maza" Ta ce "To kar maman su Hafsa ta dawo ban gama ba, labulayenta ne" "Ajiye, su hafsa idan sun dawo su wanke mata, maza ki tafi". Cikin murna ta tashi, ta tattare kayan wankin, ta shirya cikin uniform ɗin ta, ta tafi islamiyya. Duk da yau ma sai da aka zane ta, sannan ta shiga ta kai kuɗin makarantar tana ta kuka, dan ba ta ƙaunar duka sam. Sai dai duk da kukan da tayi, hakan bai hanata farincikin ganin ta koma makaranta ba. Sai dai bayan ta koma gida, Anty ta rufeta da bala'in ta tafi ta bar mata bedsheets ɗin da ta saka ta wanke mata. Jakarta kawai ta ajiye, ta hau wankin da aka sakata, bayan ta sha uban zagin tsamar nama, ita duk hakan bai dameta ba, ta kammala wankin sauran bedsheet ɗin, ta wanke kwanuka ta mayar da abincin dare. Duk ƴan matan gidan suna zaune, itakaɗai take aikinta a tsakar gidan, idan baƙo ya zo sai ya yi zaton mai aiki ce. *** Yau tun a makarantar boko, Jauhar ta ji period ya zo mata, gashi kuɗin pad ɗin nata saura ɗari da hamsin ba su gama cika ba, sai kame jikinta take yi, saboda tsoron kar jini ya ɓata ta. Da ƙyar ta isa gida, tana ta lissafin yadda za ta yi, gashi idan ta yi amfani da tsumma, lalata mata fata yake yi, ƙuraje duk su feso mata, ta rasa in da zata saka ranta. Haka ta wuni tana fama, ga uban ciwon mara, kamar tayi hauka, dan ma ta samu paracetamol a wurin Yaya saifu ta sha, ga uban aiki dan babu mai ɗaga mata ƙafa, haka nan ta saka tsumman, take amfani da shi, idan ba haka ba ta san haka za ta yi ta staining. Da magariba, tana zaune a tsakar gida, ta cinye ɗan abun da ta samu ta ci, wanda sam ba ta ƙoshi ba, duk da ita ta girka, sai lashe hannu take yi, Baba yayi sallama. Aka din ga jera masa sannu da zuwa, yana amsawa. Ya kalli Jauhar ya ce "Waliyiyya ya na ga kina suɗe hannu, ba ki ƙoshi bane?" Tayi murmushi ta girgiza masa kai ta ce "Alhamdilillah, na ƙoshi baba". Ya ce "To madalla, Allah shi ne abun godiya, akwai wani mutum da ya zo wurina yayi mini maganarki, ban sani ba, ko ke ki ka turo shi" Gaban juahar ya faɗi, ta kalli in da mama ke zaune a kan tabarma, ita ma tana cin nata abincin. Sau ɗaya saurayi ya taɓa biyota gida, mama ta ce idan wani ya kuma zuwa wurinta, ko ta bawa wani damar ya zo wurinta, sai ta kusa halakata, yayyenta ba su auru ba, ba za ta fara kawo musu maza ba, duk da dama shekarun nata ba yawa ne da su ba, haryanzu a SS2 take shekara goma sha shida, sai dai hasken fatarta ke ɗaukar idon samari ƴan bana bakwai, su biyota wai suna so, saboda kashedin mama ta koma saka niƙab. But Anty, babar su hafsa ta fito daga ɗakin ta, tana jiran ta ji ƙarashen maganar. Mama ta ce "Ba magana ake yi miki ba?" Jauhar ta girgiza kai ta ce "A'a Abba, wallahi ban san kowa ba, ban turo kowa wurinka ba" "Ƙarya ki ke yi, zaki aikata, ba abun mamaki bane ba kina halin kule-kule a waje, dan a zahiri kina da fuskar tsoron Allah, amma a baɗini ba kya ji" Anty ta ara ta yafa ta ƙarar da zancen. Baba ya ce "No, shi ma ya gaya mini, bai yi mata magana ba, ya zo ya fara samuna ne, na dai tambayeta ne kawai dan na tabattar, zan bashi dama ya fara zuwa wurinta, dan naga da gaske yake yi." Dumm ƙirjin Jauhar ya buga, ta fara zance yanzu, makarantar kuma fa, ga burinta na son yin karatu, duk da aure ba ya hana karatu, to amma idan wanda zata aura ɗin ba zai bari ba fa?. Da sauri mama ta tashi ta bishi ɗaki, tana yi masa magana "Yanzu aurar da jauhar ɗin zaka yi, ga yayenta duk a jibge, su kusan biyar babu wadda ka aurar?" Ya tsaya ya kalleta ya ce "To laɗifa, tara su zamu yi tayi ba zamu aurar ba? Tun da ita Allah ya fara kawowa sai mu fara da ita, ita ma ta huta" A take ta haɗe rai ta ce "Ban gane ita ma ta huta ba, na fuskanci duk lokacin da magana irin wannan ta tashi, sai ka nuna kamar bana ƙoƙari a kan riƙonta, kamar zaluntar ta nake ko?" Kamar yaronta ya ce "A'a bance ba" "To wallahi ba za ayi wa jauhar aure ba, ga su Sajida ba, wannan ai cin mutunci ne". Yayi mata shiru, bai sake cewa komai ba, ya ƙuduri aniyar, aurar da jauhar ko ba ta so. *** A tsakar gida ta tsaya tana ta kwaɗa sallama, daga cikin falon aka amsa mata, wata matashiyar mata ta fito. Suna ganin juna suka rungume juna, suna murna. "Zakiyya Bala, yau ke ce a gari?" "Wallahi kuwa Rahila". "Ya aka yi ki ka gane gidan nan? Kin san lambarki na rasa". Zakiyya ta ce "Ke wayata aka sace mini, tun da na canza layi na rasa lambarki nima, ai da Abba na haɗu a bakin titi, ya ce mini ai kun jima da dawowa unguwar nan, bamu da wani nisa bamu sani ba". Rahila ta ce "Allah sarki, shigo daga ciki, shegiyar ƙawata, na yi missing ɗinki fa" suka shiga suna dariya. Ta kawo mata ruwa da lemo ta ajiye, Zakiyya ta kalli gidan ta ce "Ikon Allah, nan ku ka dawo kenan?" "Wallahi kuwa, ai yanzu ba abun, tun da aka damfare shi ɗin nan, lamuran sai godiyar Allah, amma a hakan ma ai bamu tagayyara ba" Zakiyya ta ce "Gasakiya ne, Allah ya ƙara rufa asiri, ina su kursum?" "Duk suna makaranta, kin san tana level 3 ita yanzu, ina su hafsa, haryanzu babu labarin aure ko?" "Haba Rahila, yaushe za ayi auren su Hafsa ba ki ji labari ba, wallahi babu shiru, abu kamar saka hannu, har na fara zargin uwargidana, sai na ga ita ma ga nata nan biyu, Sajida da surayya, suma babu ana ta shige-shige shiru, dan ma ni da ita kar ta san kar ce, an daɗe ana gogawa taga babu riba, na sha gabanta shi ne ta sarara mini". Rahila ta ce "Subhanallah, kin ga nima ana ta fama, duk wanda ya zo kamar walƙiyya sai ya tafi, ni kuma ba zan bawa talaka aure ba wallahi" "Ba ke kaɗai ba Rahila, kin ga yaran nan, har mai suka shafa, sun yi ɗas sun zama farare, kwalliyar nan, supplements ɗin nan, na gyara dai, amma ba tsayayye duk sai shirmanmu" "Ki daina damuwa fa, lokaci ne" "Wallahi haka ne, ba ki san wani abun takaici ba, wai sai yarinyar nan, ƙanwar bayansu, jauhar ƴar bafulatanar nan da ya taɓa aura kwanaki, aka rabu tsiya-tsiya ƴar da ta mutu ta bari, wai ita wani ya ce yana so da aure, yarinyar nan sai da Laɗifa ta shiga ta fita, ko suturar kirki ba ta sakawa, wai amma a haka wani ya gani yake so, kin san ita ya bawa riƙonta" Rahila ta kwashe da dariya ta ce "Ai wasu lokutan maza ƴan wahala ne, ga in da ya dace su je, amma wani wurin suke kai kan su. Ni kaina ga nawa ɗan riƙon ya sani a gaba, ɗan gidan zahra'u tsinannen yaron da asiri baya cin sa, babu irin kurciyar dan ban saka ayi masa ba, amma abu ya gagara". Zakiyya ta gyara zama ta ce "Ke haba? Al'amin ko" "Shi, ai ya zame mini bala'i Zakiyya, ya zama riƙaƙƙen ɗan daba da shaye-shaye, za ki ji matasa suna mai dogon zamani shi ne fa" Zakiyya ta dafe kai ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ke ina jin labarinsa har a radio, dama shi ne, amma lokacin kina amarya kamar a nutse yake" "Ke rabu da ni oho masa, ni sonake ya bar gidan nan, kar ya hana mini ƴaƴa auruwa, ko ya illata wani, dan Abba da ki ke gani ɓaras ya karya mini ɗa kamar kara. Kina kallon halin da muke ciki, yanzu babu bushasha kamar da, ɗan abun da ta bari ya gada, ubansa ya fito da shi, ya ƙara jari, yaƙi wai ba zai taɓa masa kaya ba, kin ga da zai bar gida a neme shi a rasa ai ma samu mu ci, babu irin korar da ban saka ya yi masa ba, amma yaƙi tafiya". Haka suka cigaba da hirarraki, wadda galibi a kan rayuwar makaranta da suka yi, sai na iyalinsu hirrar take. Kusan sati biyu, da maganar da baba yayi, a kan wanda ya zo wurinsa a kan jauhar, yayi shiru da maganar kamar ta wuce, ya dawo da yamma, kasancewar juma'a ce, jauhar ta duƙufa tana ta shirin dutse. Kuɗinta da suka taru ba ta samu ta sai pad ba, sai ta sayo riɗi, ta ce zata soya ta juya kuɗin, idan suka taru ta saya da wuri. A tsakar gida baba ya tsaya, ya ƙwala mata kira, ta amsa ta fito ta tsuguna. Ya kalleta ya ce "Ki shirya, ki je ga baƙonki can a waje ya zo ku gaisa". Ji tayi kamar ta fyalla da gudu, ta tsaya da saurayi, ya ce mata me, ko ta ce masa me? Amma ta amsa masa, ta tashi ta shiga ɗakinta, jikinta duk yayi sanyi. Sajida ta shiga falo in da su surayya ke kallon Bollywood. "Kai kuna nan kuna kallo, baba fa da gaske yake auren jauhar zai yi muna zaune" Surayya ta ce "Kamar yaya?" "Kamar yadda na gaya muku, wallahi wai wani ne wai yake son ta" Hafsa ta ce "Da yardar Allah ba za ta yi aure ta barmu ba". Jauhar kuwa turus ta yi, tana kallon ƙatuwar motar da ke ƙofar gate ɗin gidan an yi parking ɗin ta. Zura kai ta yi tana lelleƙawa ta ga waye baƙon. Ya buɗe ƙofar motar ya fito, yana murmushi. Turus ta yi tana kallonsa, ya yi murmushi ya ƙaraso ya jingina da jikin motar, ya ce "Mayar da idon mana, kin yi mamakin ganina ko?" Da sauri ta durƙusa ta ce "Ina wuni?" "Lafiya ƙalau Faɗimatul Jauhar" Ya ɗan gyara tsayuwarsa ya ce "Na san dole zaki yi mamakin ganina, zuwa na yi na sake bayar da haƙuri, a kan incident ɗin da ya faru, na tsorata ki da na yi, na kusa buge ki da mota" Jauhar ta ce "Ai bakomai ya wuce, na ma manta" "Ai ni ban manta ba, dan sai da na koma wurin da muka haɗu, na tambayi ina ne gidanku, na samu baba muka yi magana, hankalina ba zai kwanta ba, har sai na aure ki, na kai ki gidana, na rarrasheki da kyau" Jauhar ta sunkuyar da kanta, tana jin abun wani banbarakwai. Ita gaba ɗaya ma ji take yi ya takurata. "Jauhar" "Na'am" ta amsa tana kallonsa da idanunta da suke farare tas, sai dai ba manya ne can ba. "Me ki ka ce? Ni aurenki nake son na yi, kuma nan kusa wallahi ba da nisa ba, na yaba da tarbiyarki fiye da yadda ki ke tunani". Kamar za ta yi kuka ta ce "Ai ban gama makaranta ba, ni yarinya ce kai kuma babba ne" Dariya yayi ya ce "Wow, ashe shagwaɓaɓɓiya ce har haka? To dan ni babba ne ba za a aure ni ba? Kar ki ce haka, zaɓin Allah ake nema kin ji sweetheart, ki yi ta addu'a Allah ya tabattar mana da alkhairi. Ina da mata ɗaya da yara biyar kacal, yaro ne ni haryanzu" yayi mata maganar yana kashe mata ido ɗaya. Ita kam gabanta ne ma ya faɗi, yara biyar ne kacal, ita duk wata harka da za ace kishiya, tsoronta take ji. "Kar in cika ki da surutu, bani lambar wayarki, a hankali zamu saba, kin shiga raina sosai, zan yi iya ƙoƙarina na baki kulawa dai-dai iyawa ta, kuma karatunki, in sha Allah sai kin ce kin gaji dan kanki" yayi maganar yana miƙa mata wayar ta saka masa lambarta. "Bani da waya ai" Ya ce "Ohh, ashe fa ƴar baby ce, ba ta isa riƙe waya ba, zan kawo waya in sha Allah" "A'a dan Allah kar ka kawo mini, ba ma za a bari na riƙe ba" "To ikon Allah, to ta ina zan din ga jin muryarki? Amma shikenan bai kamata na karya dokar gidanku ba, zan san abun yi na nemi iznin baba na kawo wayar. Amma baki tambayi sunana ba" Ita dai tayi shiru, tana mamakin yadda babban mutum kamar wannan, yake ta kashe mata murya. "Sunana Alhaji Mu'azzam. Ina dillancin kayan sawa, mussaman na mata, ina shigo da kaya daga ƙasashe daban-daban, kuma ni ɗan siyasa ne, yanzu haka ina da muƙmi a gwamanati, amma ba dai wannan ba, ni amincewarki nake nema, kar ki yi saurin rejecting ɗina ki yi mana addu'a kin ji zahrana" Jauhar dai ta yi gum, ita wannan tsayuwar ma kawai, kunya take bata kamar ta falfala da gudu. Haka ya gama surutansa, ba komai take fahimta ba, lissafi kawai take a zuciyarta, saura dozen nawa ta gama shirin dutse, ta kai ta karɓo kuɗin, ta cika ta soya riɗi. Kuɗin da ya miƙo mata, ya sanya ta ja da baya, tana girgiza kai. Ya kaɗa ya raya, amma fafur ta ƙi karɓa, sai haƙura yayi. Haka yayi mata sallama ya tafi, da sauri ta shiga gida, dan kuwa Alhaji mu'azzam duk ya cinye mata lokaci, ba ta ƙarasa shirinta ba, mugun kallon da ta tarar da ƴan matan gidan na yi mata a tsakar gida, ya sanya ta shan jinin jikinta, dan kuwa tuni yaran gidan suka kawo musu tsegumin irin motar da aka zo wurin Jauhar da ita. Sai jikinta yayi sanyi, ta hau tunanin laifin me tayi? Jiki a sanyaye ta ɗaukko aikinta ta cigaba. Sai dai suka din ga zaginta babu dalili, hafsa ta saka ƙafa tayi fatali da ɗan plate ɗin jauhar da take zuba dusten. Hankali a tashe ta ɗaukko tsintsiya tana tattarewa, ba tare da ta damu da son sanin dalilin da ya sa hafsan tayi mata haka ba, domin kuwa idan da sabo ta saba. Yaya saifu da ya fito daga banɗaki ne, ya ɗurawa Hafsa ashar, saboda ya ga abun da ta yi hafsa. Babarta ce ta fito tana yi masa masifa, tana kare hafsa, da mayar masa da zagin da yake yi mata. Aikuwa mama ma ta fito ta haushi da bala'in menene ruwansa da shiga abun da babu ruwansa, nan faɗa ya harƙe, sum-sum jauhar ta ja jikinta ta koma ɗaki. Da daddare bayan sallar isha'i, baba ya kira jauhar ɗakinsa, ya tambaye ta yaya suka yi da baƙonta, amma ta kasa magana, sai duƙunƙuna hannunta da ta din ga yi a hijjabi. "Jauhar" Kanta a sunkuye ta ce "Na'am baba". "Ba zan yi miki dole ba, ban bawa mutumin nan damar zuwa wurinki ba, sai da na yi bincike a kansa, na san makarantar ki ke tunani, ina mai tabbatar miki ya tabattar mini zai bari ki cigaba. Bana jin daɗin irin rayuwar da ki ke yi a cikin gidan nan, babu yadda zan yi ne. Amma idan ba kya son sa, ba zan yi miki dole ba, ki bi komai a sannu, ki yi istikhara da addu'a, na san ke mai yawan addu'a ce, da miƙa lamuranta ga Allah, ki ƙara dagewa sosai da sosai, ki nemi zaɓin Allah" "To Baba in sha Allah" "Yauwwa yarinyar kirki, Allah ya yi miki albarka, ya sa naga jikokina ƴan farare masu kyau kamar jauhar ɗina" rufe fuska tayi ta ƙunshe fuskarta tana murmushi. Tun da ya shigo layin, wasu daga matasan layin ke darewa, suna ɓuya, ko a jikinsa, tafiyarsa yake yi cikin hanzari da ƙasaita, sumar sa ta cika masa kai, ya aske wani wurin ya bar wani, irin cikakken mara jin nan. Kai tsaye ya buɗe ƙofar gidan, ya kunna kai cikin gidan. Babu sallama ba komai, ya kutsa cikin falon in da suke zaune suna karyawa. Abbu ya ɗaga kai ya kalle shi, ya ce "Uban me ka zo yi mini gida? Me na gaya maka a kan zuwar mini gida?". Ya sunkuyar da kai ya ce "Ganinka na zo na yi na gaisheka" "Ba na buƙatar gaisuwarka Al'amin, ai tun da ka zaɓi watsewa a duniya, ka yi fatali da tarbiyarka nima na sallamaka, ka koma wurin abokanka ƴan wiwi da suka fi ni a wurinka. Kalli tsinannen askin da yake kanka, ka zo mini banda warin wiwi babu abun da ka ke yi, sanna ka ce ka zo gaishe ni? Ai ni na barwa duniya kai ka tashi ka bar mini gida" Yayi shiru yaƙi tashi, kuma ya ƙi magana, sai murza zoben azurfar hannunsa da ƙarfi da yake yi, zuciyarsa na zafi. Rahila ta ce "Dan Allah ka fita Aminu, wannan warin da ka ke yi, zan iya amai wallahi, kuma ni idan ina ganinka tsoro nake ji wallahi, tun da kullum a buge ka ke kar ka illatani ko yarana a banza" tamkar tana magana da dutse, haka yiyin gingirin gim, bai motsa ba. "Ba magana ake yi maka ba?" Yayi masa maganar cikin tsawa. Al'amin ya ɗaga idanunsa, da suka yi ja fiye da lokacin da ya shigo, ya ƙara matsawa kusa da mahaifiyar, ya zuba masa ido sannan ya ce "Na san ina wari, na san kullum a buge nake, a kowane lokaci zan iya ɗaukar makami na hallaka duk wanda ya yi gaba da gaba da ni, ko wanda bai ji ba bai gani ba. Wasu lokutan ma banbancina da mara hankali kaɗan ne, na san ba na jin magana ko kaɗan, bana tsoro ko shakkae aikata duk wani abu da zuciyata ta raya mini, amma idan ban zo wurinka ba wurin wa zan je? Da haka nake? haryanzu ban san laifina a wurinka ba Abbu, zan yi ƙoƙarin daina zuwa gidan nan kamar yadda ka buƙata, ko aka ce maka ana buƙata, amma idan na daina na daina kenan har abada wallahi! Ka huta lafiya" yayi maganar yana shafar saman hannun mahaifinsa. Yana miƙewa zai wuce, yayi ball da flask ɗin ruwan zafin da yake tsakiyar wurin, da kwanukan. Gaba sai da suka razana. Ta ce "Ka gani ko?" Shiru mahaifin Al'amin yayi, ya tashi da sauri ya bi bayansa, sai dai yana fitowa daga falon, ya ga an jefo Abba, babban ɗan Rahil, ƙaton saurayi amma kamar an watso shara. Ko ba a gaya masa waye ba, ya san aikin Al'amin ne, Abba kuwa bajewa yayi, ko shurawa ba ya yi, rahila ta fito tana kururwa. Abbu ya leƙa waje da sauri, a can ƙarshen layi, ya hango Al'amin, ya zare wuƙa yana ta zuba sauri. Ya rufa masa baya, yana ƙwala masa kira, amma ya ƙara sauri har da gudu, ya bar layin. Ayshercool 08081012143 18 🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143* Ganin Aminu ya ɓace masa, ya sanya ya koma gida da sauri, rahila sai kururwa  take yi, tana jijjiga Abba. Ƙannensa mata su azima, suka kewaye shi suka hau kuka. Abbu ya ɗebo ruwa, ya din ga zubawa Abba, har Allah ya sa ya buɗe ido. Cikin kuka take cewa "Ka gani ko? Ba zaka taɓa yadda da ta'addancin ɗanka ba, har sai ranar da ya kashe mini ƴaƴa, me yayi masa zai yi masa wannan ɗibar karan mahaukaciyar ya watsar? Wallahi na gaji, ina ga tafiya zan yi na bar maka gidan nan kai da ɗanka, na rasa uban me yaron nan yayi masa, ko dan ba kai ka haifi abba ba, ya tsane shi daga shi har nazifi ni ban sani ba. Ni ba abun na kai shi ƙara wurin hukuma ba, ba sa yi masa komai sai dai a sako shi, ni na gaji". Abbu ya ce "Dan Allah ki daina wannan maganganun, bari na samo mota, mu kai shi asibiti" Abba kuwa ko magana ya kasa, Nazifi ne ya taimaka aka fita da Abba zuwa mota. Al'amin kuwa da ya tabattar da ya tserewa Abbu, ya samu wani lungu, ya jefar da wuƙar hannunsa, ya samu wuri ya zauna, yana ƙoƙarin haɗiye wani abu mai tsananin ɗaci da zafi a maƙogwaronsa, ji yake kamar numfashin sa zai ɗauke, babu abun da zuciyar sa ke raya masa, banda ya kashe matar Abbu wato rahila ya huta. *** Gidan babu kowa, duk yaran sun tafi makaranta, mama tayi sallama a falon zakiyya. Ta amsa tare da fitowa daga bedroom ɗin, tayi miƙa ta ce "Lafiya kuwa?" "Au bacci ma ki ke yi? Lallai kam, to magana na zo mu yi" Zakiyya ta ce "Ok, bisimillah zauna mana" Ta nemi wuri ta zauna, ita ma ta zauna. Mama ta kalleta ta ce "Kin san waye yake son Jauhar kuwa?" "A'a sai kin faɗa". "Ɗan familyn mai atamfa ne" Waro ido Zakiyya ta yi, har tana neman faɗowa daga kan kujera, ta ce "Wani mai atamfar?" "Waɗanda dai ki ka sani,ba ma wannan ba shi zai tsaya takarar majalissar tarayya a yankinsu, jiya na tutsuye shi, yake gaya mini, ga kasuwancin atamfofi da lesuna da yake sayarwa, daga ƙasashe daban-daban yake order kaya, na din ga bugun cikinsa yana gaya mini, wai zata yi karatu idan tana so, idan business take so zai ba ta jari, idan ma zaman gida take so, ayi din ga yi mata komai, duk zai iya kuma nan kusa yake son ayi auren". "Bantan uba, namu ƴaƴan suna zaune za ayi hakan, muna me?" Mama ta ce "Hmm, ni fa na daɗe ina hana faruwar wasu abubuwan, rannan daga aikenta gidan Hajiyar lamin, wai ɗan wan maigidan ya ganta, ya ce ayi masa hanyar aurenta, uban yaron fa sanata ne a Adamawa, hauka nake? Na toshe na hana, na din ga aika su surayya, da walida amma ko kare a familyn babu wanda ya sinsuna su. Lokacin da suka yi sauka ma, babu kunya wai chairman yana son ta, tun ba ta kai haka ba ma, na ce ba za a lalata mata tunani ba, karatu take yarinya ce, na rasa wannan masifar". "Mun shiga uku, meyasa kowa sai ita? Kuma duk masu kuɗi, namu yaran fa?". Mama ta ce "Wannan shegiyar farar fatar suke yi wa ai" "Wace farar fatar? Su ma duk ba suna shafa mai ba, manyan zaratan ƴan mata, sun sha mai da kwalliya amma ace su duk shiru sai ita?" "Shiyasa tun jiya ban yi bacci ba wallahi, na saƙa wannan na kwance wancan, dole fa a rusa wannan maganar ma" Zakiyya ta ce "To yanzu menene shawara? Wallahi na rasa abun cewa, ko malamai zamu shiga ne?". "Babu lallai yayi tasiri, na fuskanci ƙashin masu arziki ne da ita, amma mu cigaba da shawara kafin faruwar abun". Zakiyya ta ce "In sha Allah " Mama ta miƙe ta ce "Sai na ji ki". *** Cikin ikon Allah Abba ya warware, babu abun da ya same shi, sai dai ya bugu, ya yi ta fama da jiri, sai da ya kwana uku a asibiti, aka sallame shi. Rahila ta cigaba da ɗagawa Abbu hankali a kan Al'amin, a kan lallai ya kai shi wurin hukuma, a san yadda za ayi da shi, kafin ya yi mata kisan gilla ita da yaranta. Gaba ɗaya maganganun Al'amin sun yi tasiri a zuciyarsa, amma kuma wani ɓangaren, Rahila tana da gaskiya, al'amin barazana ne a gare su, saboda yadda sunan mai dogon zamani, yayi ƙaurin suna a bakin mutanen unguwa, ba iya unguwar ba, har gidajen radiyo, duk wani faɗan daba da zai tashi a arear rukunin unguwannin to sai an ambaci mai dogon zamani wato Al'amin. Ƴan sanda har sun gaji da kama shi, idan an kama shi ma, ƴan siyasa sai sun saka an sako shi, daɗinta ɗaya ba ruwansa da taɓa kowa ko kayan kowa, sai ƴan daba da jami'an tsaro da su yake faɗansa. Bayan Jauhar ta dawo daga makaranta, mama da Anty suka sakata a gaba, suna sake yi mata tambayoyi a kan Alhaji mu'azzam, Jauhar ta rasa me za ta ce musu, dan ita ba komai ta sani a kansa ba, dan tun da ya zo sau ɗaya, bai sake zuwa ba, dan haka ta din ga ce musu ba ta sani ba. Aikuwa suka din ga zaginta, tare da kiranta munafuka. Suka gama zaginta, ta cigaba da sabgoginta. Yaya tijjani ya shigo, wanda shi ne babba a gidan, ya shiga wurin mama, jauhar ba ta san hawa ba, ba ta san sauka ba, ya kamata ya zane a yammacin nan, wai an ce masa kule-kulen maza take yi. Ihun jauhar ne ya sanya yaya saifu shigowa, ya tarar TJ yana mata bala'i, wai tana kula maza. "Haba yaya TJ, idan ba ta kula maza ba, kai za ta kula? Ko za a jiƙata a ruwa a sha ne? Da iznin baba fa ya zo wurinta idan ma a kan wannan mutumin nan" Mama ta ce "Rufe mini baki, kai da ba ka san me duniyar take ciki ba, yadda maza ke lalata yaran mutane yanzu, idan aka sake lalata ta kawai zai yi ya gudu, kuma fuska ya gani shiyasa ya biyota har gida, da ba ta bashi fuska ba ba zai zo ba. Idan da gaske yake auren zai yi, duk ga mata nan da suka fita komai sai ita. Saifu kawai ya girgiza kai ya fice, ransa ba ya yi masa daɗi, da irin riƙon da ake yi wa ƙanwarsa a gidan nan, shikenan maraici sai ha zama makamin cutar da bawa?. Har jauhar ta gama girkin dare, kuka take yi, dan ta daku sosai da sosai, fatarta duk tayi ja. Baba da ya dawo, bai san me aka yi ba, na dukan Jauhar. Ɗan autansu ne wato amir, ya shigo ya ce "Jauhar ana kiranki a waje, in ji wannan mai motar, kin ga har ya bani kuɗi dubu biyu". Anty ta ce "Ba zata je ba, je ka ce ba ta nan, ki mayar da kai ki gama sauran aikace-aikacen ki, idan kuma baki da abun yi, ki zo ina da shi ki yi mini". Baba ya fito da kansa ya ce "Amir, je ka ka ce tana zuwa, Waliyiyya, ajiye duk abun da ki ke yi, ki je ki sallami baƙonki". "Amma Alhaji..... "Amma me? A kan me zaku hana yarinya zance, maganar aurensu fa za a fara kwanan nan, da yaya za su fahimci juna?". Jauhar kamar ta ce wa Baba ba zata je ba, dan tana tsoron a sake saka yaya TJ ya dake ta. Amma ta kasa magana, ta zura hijjabinta, ta fita. Tun kan ta fita ta fara jiyo ƙamshin turaren sa, kamar wancan karon ta durƙusa tana gaishe shi. Sai dai bai amsa ba, ya ce "Na yi missing ɗinki Jauhar, sai dai na baki lokaci ne, dan kar na dame ki. Yaya ake ciki kin yi mana addu'ar? Kin fara so na?" Maimakon ta bashi amsa, sai ƙifta ido take yi, tana waiwaye kar TJ ya zo ya ce zai sake dukanta, tun da ta tsaya da wani ne ba sa so. Ya ɗora da cewa "Dama baba ne ya ce na ɗan baki lokaci, to kuma ga tafiya ta kamani babu cikkaken shiri, na ce a kawo mini kuɗin aure, kafin na tafi, amma na ga bari na ji ta bakinki, kar na yi miki shigar sauri" Tayi shiru kamar ba da ita yake ba. "Baby yangar nan tana yawa fa, dan Allah ki yi mini magana na ji nutsuwa mana" yayi maganar yana dawowa kusa da ita ya tsaya. "Jauhar ki yi magana mana" "Allah ya zaɓa mana abun da ya fi alkhairi" ta faɗa a hankali. Ya ce "Kin amince zaki aureni?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "Wow, anya ba zan  ce a ɗaura mu tafi chinan tare ba?" Ta ce "A'a, dan Allah a bari na gama makaranta, mun kusa yin WAEC". Alhaji mu'azzam ya ce "Na so ace zan iya yi miki hakan, amma ba zan iya jurewa ba, kar wani ya rigani, ko da na tafi ina can, iyayena zasu zo ayi maganar, da na dawo sai maganar bikinmu, i will be with my little baby amarya very soon in sha Allah" Tayi murmushi cikin jin kunya, tana murmushi. "Jibi in Allah ya kaimu fa zan tafi, babu tsammani tafiyar ta zo, me zaki gaya mini kafin na tafi, da zan din ga tunawa da ke, kin ƙi yarda na baki waya, balle mu din ga waya ina jin daɗi. Yanzu me zaki ce mini?". Ta ce "Duk lokacin da ka tuna ni, ka yi mini addu'a" "In sha Allah amaryar mu'azzam, zan din ga yi mana, daɗin auren mace mai addini kenan" Ya din yi mata hira, har ta ɗan sake tana yi masa murmushi. Ita dai ba ta sani ba tana son sa ko ba ta son sa, duk da ya girme mata, ya iya magana, ya sauke shekarunsa dai-dai da nata, ga ƙamshin turaren sa daɗi yake yi mata, dan a hakan yadda take fama, idan ta samu ƴan kuɗi, baka rabata da turare. Daga kan Surayya zuwa walida da hafsa, babu wadda ba ta fito ba, da niyyar za su fita yin wani uzurin, kuma babu wadda ba ta gaishe shi ba, sai dai gaba ɗaya hankalinsa da nutsuwarsa yana kan ƴar bainun gabansa wato Jauhar. Da zai tafi, sai da ya haɗe rai sosai, sannan ta yarda ta karɓi kuɗin da ya bata. Sai da ya tabattar ta shiga gida, sannan ya tafi. Ɗaki ta je ta bawa baba duk abunda ya bata, kuɗi masu yawa, mama ta din ga masifa, kamar ta ari baki, da sunan kula da tarbiyyar Jauhar. *** Al'amin yana kashingiɗe yana busa wiwi, yana kaɗa ƙafarsa ɗaya, yana jin sa a sama, dai-dai da kowa, sai dai busa hayaƙin yana bashi nishaɗi, yana jin daɗin hakan. Wuƙar gefensa ya ɗauka ya zauna sosai, ya karta ta a ƙasa, ya gyaɗa kai sannan ya ɗago ya ce  "zan shiga ƙofa, zan tayar da tarzoma, zan je ɗaukar fansa" "Wurin madakin dai?" Walid yayi maganar yana kallon sa. "Koma wurin waye, ka manta abun da suka yi mana kafin na je prison?" Walid ya girgiza kai ya ce "Ban manta ba" "Zamu ɗauki fansa, madaki kuma ban ce kowa ya taya ni ba, faɗana ne nikaɗai wannan". "Shikenan yaushe zamu shiga?" "Shammatar su zamu yi, zan yi muku magana" Ya koma ya kashingiɗa, ya cigaba da zuƙar wiwi. ***** Tun da Allah ya sa Alhaji mu'azzam ya tafi, Jauhar ta manta da babinsa, sai dai in mutanen gidan sun ɗaukko hirarsa, ita da yake zuwa wurinta ma ba ta zancensa kamar yadda suke yi. Babbar murnarta ita yanzu, ganin yadda kantunta yake ƙarewa da wuri, duk da ana yi mata mugunta a gidan, yaya saifu ya ƙara mata jari, ya bata dubu ɗaya. Ɗan kuɗin da take juyawa, da na riɗin, da na shirin dutsen, bai fi dubu biyu da ɗari biyar ba, amma murna take yi da hakan, jin kuɗin take da yawa, dan ƴar hamsin ɗarin da take bi na riba, ba ƙaramin daɗi yake yi mata ba, dan nan da nan ta tara kuɗin pad, har ta fara tarin kuɗin makarantar islamiyyarta, kan lokaci yayi ta zo tana nema. Yau an tashi daga islamiyya, ta sayar da riɗinta tsaf, dama da ɗaurin shirin dustenta, ta fito daga aji, tana lissafin tayi maza ta kai musu, ta karɓo wani. Ko da ta fito wajen gate ɗin makarantar, matasa suka gani suna guje-guje, wai faɗan daba ake yi, mai dogon zamani ya shigo ɗaukar fansa. Jauhar ko a jikinta tayi gaba, tun da daga in da ake gudun bayansu ne, dan haka tayi gaba abun ta, ta nufi hanyar gidan da take karɓar shirin. In da take bin shiru babu mutane ma, tana shiga layin gidan shirin, ta ɗaukko robar riɗinta, ta ciro kuɗin cinikinta, ta hau ƙirgawa murmushi ta saki, tana jin daɗi, ta fara tunanin tambayar kuɗin aya gwangwani biyu, ita ma ta din ga soyawa da gishir tana sayarwa. Hankalinta ne yayi mummunan tashi, bayan da tayi baƙin ganin da ba ta farga da shi ba sai yanzu. Hannunsa riƙe da wani mutum, da ba ta da tabbacin yana da rai ko babu, da wuƙa a gefen cikin mutumin, hannunsa duk jini, kuma shi ma da yake riƙe da mutumin da take kyautata zaton kashe shi ya yi ƙafarsa sai zubar da jinin take yi. Tun da ta shigo layin ta fara lissafa kuɗi, ya ɗaga kai ya ganta, amma ita sam ba ta ganshi ba, hankalinta yana kan lissafin kuɗin da yake hannunta, sai da ta je tsakiyar layin, ta kusa zuwa daf da shi sannan ta farga. Zuciyarta ce ta fara wani iri razanannen bugu, gashi ta kasa ko da motsa ƙafarta, balle ta cirata ta gudu, ba ta taɓa ganin mummunan tashin hankali ba tun da take a rayuwarta ba sai yanzu, ita ko film ne ta ga ana kashe-kashe, ko harbe-harbe bata kalla, kodayeke ita kallo ma bai dameta ba, amma sai yau gata ga gawa da jini. Ba tare da ta yi tsammani ba, wani irin ƙarfi ya zo mata, ta taƙarƙare iya ƙarfinta, ta kurma wani irin uban ihu, ta yinƙura da niyyar ta gudu, sai dai tsananin bugun da zuciyar ta take yi, ya sanya numfashinta kasa daidaituwa a ƙirjinta, kuma ta gaza ɗaukar nauyin jikinta, dan haka ta faɗi a wurin a sume, robar da cinikin, da jakar islamiyyar duk suka watse a wurin, gefen kwata. Duk da wannan uban ihun da tayi, babu wanda yayi ƙoƙarin buɗe ƙofarsa ya ga mai yake faruwa. Duk da dama, gidaje biyu ne kacal a layin, sauran duk bayan wasu gidajen ne a cikin layin. Tsaki ya ja, ya mayar da idonsa kan liti, da yake numfashi sama-sama. Ya kalli ƙafarsa da take ta zubar da jini shi ma, saboda saran da aka yi masa. Ya kwantar da liti, ya tashi ya tafi kan jauhar, ya kai hannun sa kan hancinta, ya ji tana numfashi. Ya kamo hannunta, ya riƙe tsintsiyar hannunta, ya ji zuciyarta na wani irin bugu, da saurin gaske. Kamar ya ɗauki tabarma, haka ya ɗauketa daga kan hanya, ya kwantar da ita a tsallaken kwatar, ya tattaro kayanta ya haɗe mata wuri guda, sai dai uniform ɗin ta, duk sun ɓaci da jinin da yake zubarwa. Wald ne ya ƙaraso layin da sauri, shi ma hannunsa riƙe da wata sharɓeɓiyar wuƙa tana zubar da jini, ya ƙarasa in da Al'amin yake harya fara ganin jiri, saboda jinin da ya zubar. "Subhanallah, waye yayi gangancin yankarka?" "Ƙyaleni, ka kira su baffan?" "Eh, suna bakin titi da ɗan sahun" Ya miƙe ya saɓa liti da yake zubar da jini a kafaɗarsa. Walid ya ce "Kawo shi, na ga kamar jiri ka ke yi mu ƙarasa". Ya ce "A'a bar ni da shi, zan yi wa honorable waya, ya aika mana ƴan sanda asibiti, waccan yarinyar, ka buga ɗaya daga gidajen layin nan, su fito su kaita Asibiti, ta tsorata ne, idan kuma ba haka ba za ta yi musu mushe a wurin, saboda zuciyarta na bugawa da sauri sosai" Walid ya ce "Wai wa yake ta wata yarinya, kai kaɗai zaku tafi asibitin, kalleku fa jina-jina" "Mai rai ce fa, idan ba su buɗe ba, ka haura gidan kawai, ka saka su buɗe, yanzu idan muka tafi da ita zai zama wani abun daban" daga haka yayi gaba, ya nufi barin layin. Walid ya yamutsa fuska, ya samu ɗaya daga gidajen, ya din ga wani irin bugu, kamar yaƙi. *** Cikin tsananin hanzari ta yinƙura, za ta diro daga kan gadon da take, tana faɗin"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, dan Allah ku taimake ni, zai kashe ni" Cikin azama baba ya riƙe ta, ƙoƙarin ture shi take yi, ta saukko daga kan gadon. Baba ya ce "Jauhar, buɗe idonki, ki kalleni ni ne ki nutsu" sannu a hankali ta buɗe idonta, ta kalli baba, ta juya ta kalli su mama da Yaya saifu da suke wurin, sai malam jamilu da malam hamza. Jikinta ya hau wata irin tsuma, ta dinga fizge-fizge tana ƙoƙarin fizge robar ruwan hammunta. "Ke ki nutsu mana, meye haka ne ana yi miki magana" mama tayi maganar tana haɗe rai. Ta girgiza kai ta ce "Mama tsoro nake ji, wani ya kashe fa, dan Allah ku ɓoye ni zai kashe ni nima, ganinsa nake yi a idona, dan Allah baba ku tafi da ni tsoro nake ji" tayi maganar tana ƙoƙarin tashi tsaye. Baba ya ce "Wai shi wa?" Cikin kuka ta ce "Ban san shi ba, kawai gani nayi dai ya kashe wani yana kallona, nima na san zai biyoni ya kashe ni". Baba ya ce "To ai babu wani wanda aka gani an kashe, ke kaɗai aka gani a layin a sume". Anty ta ce "Uban me ma ya kai ki can, in da ba hanyar gida ba?". "Shiri na je karɓowa" "To ubanwa ya aike ki?" Baba ya ce "Dan Allah duk a daina wannan maganar, yanzu a bari ta samu nutsuwa". Ƙoƙarin kwantar da ita Baba yake yi, ta kalli jikin uniform ɗin ta, ta ga jini, ihu ta sake yi, tana faɗin "Meya same ni, baba kalli jini a jikina, na gaya maka nima kasheni zai yi, kalli jini fa wataƙila ma na mutu ne". A take wani abu ya ɗarsu a zuciyar mama, tayi wani shu'umin murmushi, yaya saifu kuwa likitoci ya kira, aka sake yi wa jauhar allurar bacci, dan gaba ɗaya nema take ta zare. Malaman islamiyyar suka yi wa su baba sallama, malam Jamil dama a kusa da layin da take zuwa karɓar shirin yake, yana yawan ganinta, wataran shi yake korata makaranta ko gida, tun da ya fuskanci halin da take ciki, yake ƙyaleta, dan watarn har gidansu take shiga, ƙannensa ƙawenta ne. Shi ya din ga bawa baba baki, da bashi tabbacin jauhar ba yawo take tafiya ba, kamar yadda mama ke ta iƙrari. Baba ya ce "Ni ma na san jauhar ba ta yawo, wannan abun da ya faru ma tsautsayi ne, Ubangiji Allah ya kiyaye gaba" suka yi sallama su malam jamil suka tafi. Kusan awanni biyu, jauhar ta sake farfaɗowa, sai dai wannan karon da sauƙi, ba cikin razani ta farka ba kamar da farko. Likita ya zo yana sake dubata, Mama ta ce "Likita kun dubata da kyau kuwa, wannan jinin na jikinta ba fyaɗe ƴan daban suka yi mata ba?" Dummm! Ƙirjin Jauhar ya buga, ba ita ba hatta baba sai da gabansa ya faɗi, suka kalli mama a tare. Likitan ya girgiza kai ya ce "No, bana tunanin hakan, razani ne kawai". "To amma meya kawo jini jikinta?". Likitan ya yi shiru yana kallon jauhar. Baba ya ce "Likita ka yi magana mana" Jikin jauhar ya cigaba da rawa, tana nanata fyaɗe a zuciyarta, amma kuma da gaskiyar mama, meyakawo jini jikinta?. Likitan ya ce "Zaki iya tuna abun da ya faru?". Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Na shiga layin kawai na ga ya kashe wani, da wuƙa a cikin sa, shi ma ƙafarsa tana zubar da jini" "Kin san shi ne? Kin taɓa ganinsa?" Ta girgiza kai alamar a'a Ya ce "Zaki iya tafiya?" Ta jinjina masa kai alamar eh. Ya cire mata ruwan sannan ya ce "Saukko ki biyo ni" ta yinƙura ta sauka daga kan gadon, ta bi bayan likitan, zuwa wani ɗakin daban, ya kira wata nurse ya ce ta duba masa jauhar, amma jauhar fafur ta ce ba zata buɗe jikinta ba, sai ma ta hau kuka. Nurse ɗin ta din ga lallaɓata tana yi mata tambayoyi, ta saka ta ciro mata phant ɗin ta, ta duba ta ce wa likitan ba abun da aka yi wa jauhar ɗin mai kama da fyaɗe. Wataƙila da ta suma ya taɓa ta, tun da ta ce shi ma da rauni a jikinsa, amma ba dai fyaɗe ba. Likita ya koma ya yi wa baba bayani, baba ya din ga hamdala, mama ta ce likitan ƙarya kawai yake yi, babu yadda za ayi, ta samu jini a jikinta, idan ba fyaɗe aka yi mata ba. Likitan ya ce "Amma dai ba ƴar ki ba ce hajiya, da taki ce ba zaki yi mata wannan mummunan fatan ba, bani da wata riba da zan ci, idan na yi muku ƙarya, kuma babu yadda za ayi ayi mata fyaɗe ku kawota a haka, ba wani rauni ko alamu na fin ƙarfi, dan babu ɗan iskan da zai yi wa yarinya fyaɗe ya tsaya mayar mata da kayanta a tsakiyar layi, kamar yadda muka karɓi report" Baba ya ce "Doctor, a bar zancen ma gaba ɗaya, ni dai na gode sosai da sosai, na gode Allah da babu abun da ya sameta, za a iya sallamar mu yanzu?". Ya ce "Eh, yanzu zan sallame ta". Aka rubuta musu sallama suka tafi gida. Maƙwabta suka din ga shigowa yin jaje, saboda labari ya cika tsukin, faɗan daba ya rutsa da jauhar, an tsintota can a sume. Sai dai duk wanda ya zo, sai su mama sun bashi labarin, cewar cikin jini aka tsintota kuma jikinta babu rauni, ana kyautata zaton ko sun yi mata fyaɗe. Jauhar hankalinta ya kasa kwanciya, ta din ga tunani daban-daban, ko da ƙarancin shekarunta, a science class take ss2, kuma tana zuwa islamiyya ta san duk wadda aka yi wa fyaɗe sai ta ji wani sauyi a tare da ita, amma ita ba ta ji komai ba, babu wani abu da take ji na sauyi a tare da ita. Tun tana damun kanta, har ta watsar, sai dai ƙasan zuciyarta tana jin zafin abun da su mama suke faɗa, dan idan ta fita har tambayarta ake yi, wai da gaske an yi mata fyaɗe?. Har fita ta so ta fara gagararta. Sati biyu da faruwar lamarin, Baba ya zo ya sanar musu da cewa, iyayen Alhaji mu'azzam za su kawo kuɗin auren jauhar. Hankalinsu yayi mummunan tashi, daga su har ƴaƴan su. Suka ƙara tsananta tsangwama da kyarar jauhar. Duk da tana da matuƙar juriya, da kawar da kai, har abun ya fara effecting ɗin ta. Bai sanar da su lokaci ba, sai ranar da za a kawo ya sanar da su, hankalinsu ya ƙara tashi, sai dai ba su tsinke da lamarin ba, sai da aka kawo kuɗi masu yawan gaske. Anty ta kira Rahila, cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali take gaya mata, tare da tambayarta ko akwai wani zazzafan malamin ta haɗa su, a samu a watsa lamarin. Rahila ta ce "Wallahi ni kaina a cikin matsala nake Zakiyya, yaron nan ya zame mini bala'i fiye da koyaushe, idan ya ga dama fa cikin gidan yake zuwa ya kwana a tsakar gida, gaya miki ne ban ba, sai da muka kwanta a asibi, ya ɗaga Abba ya buga da ƙasa saboda babansa ya hana shi zuwa gidan, gashi kamar ya fara jin tausayinsa, wallahi kamar na bawa tsinanne guba ya ci ya mutu" "Innalillahi, rahila menene abun yi? Ni fa sonake maganar ta watse, a dawo mutumin ya auri hafsa". Rahila ta ce "Aikuwa kin yi dabara, ina da wani malami, wurinsa nake son komawa, ina jin daɗin aikinsa sosai da sosai, duk da su ma malamn yanzu duk sun zama ɓarayi, su ci maka kuɗi babu biyan buƙata, amma nasa babu laifi". "Wallahi kuwa, saka mana rana, ko da tsiya da masifa, lamarin ya dawo kan hafsa". "Idan a shirye ki ke, kawai ki zo mu je, ba a bori da sanyin jiki" Suka yi sallama a kan haka, ɓangaren mama ma, tuni ta zari mayafi ta tafi nata wurin malamin, a kan lallai al'amarin nan kar ya yiwu. Haka ita ma anty ta shirya, ta tafi gidan rahila. Ita kuwa jauhar, addu'a take ta yi, Allah ya sa mutanen unguwar su manta da sharrin su mama da suka yi mata, na cewar fyaɗe aka yi mata. Maganar kawo kuɗin auren duk bai wani dameta ba, ita gaba ɗaya ba ta jin dadin rayuwar ma gaba ɗaya, gashi har a lokacin tana yawan tsorata, idan ta tuna abun da ta gani, haka take ganin abun a mafarki, sai dai tayi ta addu'a tana fatan Allah ya yi mata tsari da wannan mutumin mara imani. Malamin ya gama surƙullensa, ya kalli su zakiyya ya ce "Za a iya watsa lamarin amma fa kafin dawowarsa, muddin ya dawo, babu yadda za ayi". Zakiyya ta ce "Malam tayaya kenan?" "Ko dai a aura mata wani, ko kuma a kasheta" Tayi jimmm ta ce "Kisa kuma malam, a'a gaskiya ban da kisa, muguntar tawa ba ta kai nan ba, ni fa burina kawai ya auri ƴa ta". "Ta yaya zai aureta, alhalin yana ganinta?" Rahila ta ce "Sai a juya masa tunani mana malam". "Za a iya juya masa tunani, amma ba zai juyu yadda ake so ba, abun zai sake shi da wuri, dan su ma masu kuɗin ba da ka suke zaune ba, kuma maganin ba zai yi aiki a kansa ba, dole sai ya dawo ƙasar nan, zan haɗa laƙanin, ya manta da wannan ya auri wadda ku ke so, amma muddin ya dawo yayi tozali da wadda yake son ɗin, ƙasa ta nuna mini ba zai yiwu ba" Zakiyya ta ce "Tirƙashi! Ana wata ga wata, ga ƙoshi ga kwanan yunwa" Rahila ta ce "Malam mun gode, idan mun yanke shawara zaka ji mu, tashi mu je ki ji ina da shawara" Suka sallami malamin, suka tashi suka fito, ta kalli rahila cikin damuwa ta ce "Wace irin shawara ce da ke?" "Shawara ce mai kyau, amma ina ga mafita ce, tun da damuwar mu kusan ɗaya ce, me zai hana a haɗa ta aure da wannan fitinannen yaron na gidana, kin ga kun huta na huta, su je su ƙarata, ya bar ni da mijina da ƴaƴana". Zakiyya ta buɗe baki ta ce "Ta yaya? Babanta kuwa zai yarda?" "Ke dalla can, shiga zaki yi ki fita, idan ba haka ba wallahi daular da ki ke kallo ta gagareki, kin ga mun jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya". "Wallahi maganarki gaskiya ce rahila, zan yi magana da matar gidan, ta fi ni iya sarrafa shi yadda take so a kan yarinyar, zan je mata da zancen, ayi a ƙarƙare kan wancan ɗin ya dawo". "Yauwwa, amma fa kar ki gaya mata wurin malami ki ka je" Zakiyya ta ce "Hauka nake zan gaya mata haka? Ke dai ki saurare ni kawai" "To shikenan, sai na jiki, yadda ku ka yi ki sanar da ni da wuri, nima zan wa babansa magana" suka yi sallama zakiyya ta tafi da ƙarfin gwiwar ta. Ayshercool 08081012143 19 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cike da ƙwarin gwiwa, zakiyya ta tafi gida, tare da hasaso daular da za su shiga, idan hafsa ta auri Alhaji mu'azzam. Al'amin kuwa yana zaune ya miƙe ƙafarsa, da ta sha bandeji, hannun sa ɗaya riƙe da kofin shayi yana sha a hankali. Walid ya miƙa masa buredi ya ce "Wai yaya aka yi har yaran nan suka samu suka sareka ne? Ni fa haryanzu mamaki nake yi" Al'amin ya ce "Liti suka rufarwa da sara, shi na je karɓowa, saboda sun ga suna da yawa, shi ne nima suka yi tunanin za su yi mini taron dangi" yayi wani irin murmushi yana kallon walid. "Murmushin me ka ke yi kuma?" Ya ajiye kofin ya ce"swizalan ɗina ta sha jini sosai, wannan yankanma, ban lura yaron ya taho ba ne, yadda nake ji na anya ba wasan dambe zan fara ba walid. Idan na kwana biyu ban motsa ba, idan na tashi motsawar ba na iya riƙe kaina fa". Walid shi ma yayi murmushi ya ce "Ai ƙarfi ya yi maka yawa aminu, ka shiga dambe abun ba zai yi mana kyau ba, daga karate zuwa dambe, amma da sauƙi jikin ai ko?" Ya kalli ƙafar ya ce "Alhamdilillah, da sauƙi sosai, jibi za ayi aikin honorable, zai je campaign fa" Walid ya ɗan tsuke fuska ya ce "Akwai hatsari fa a aikin nan". "Ai ban ce wani ya tayani ba, nikaɗai zan yi abuna" Walid ya girgiza kai ya ce "Sorry, ba zaka yi kai kaɗai ba, amma da rauni a jikinka, ba ka warke ba". "Ba ruwanka da ciwona, zan yi abuna a haka" walid ya girgiza kai, dan ya san ko me zai ce, bai isa ya hana Al'amin abun da yayi niyya ba. *** Kamar zakiyya za ta tashi sama dan sauri ta ƙarasa gida, saboda rahila na bata shawarar nan, ta ji shawarar ta kama zuciyarta, kuma taga hakan ne kawai mafita, ayi ayi jauhar ta bar gidan kafin Allhaji mu'azzam ya dawo, wataƙila ita ke tsokanewa samarin kirkin ido, ba sa ganin nasu ƴaƴan sai ita. Ko da ta koma gida a can ta tarar da mama, ita har ta dawo tuni. Ta ja ta ɗakinta, ta ce "Na samo mafita fa, amma ban sani ba ko zata yi miki?" Cikin zaƙuwa mama "Wace mafitar ce, ina jinki" "Me zai hana mu san duk mai yiwuwa, a aurar da jauhar, kafin Alhaji mu'azzam ya dawo, tun da dama sai ya dawo, za a tsayar da lokacin bikin". Mama ta ce "To wa za a aurawa kafin ya dawo ɗin?". Anty ta ce "Ba zai gagara ba, sai dai shawo kan Alhaji ne aiki" "Wane irin aiki kuma? Babu wani aiki, ni a wurina ba aiki bane ba, wa ki ke gani yakamata ta aura". Zakiyya ta muskuta ta ce "Kin san dai muka bari ta auri wani mai danshi, daga ni har ke babu wanda za ta saurara, tun da bamu muka haifeta ba". Mama ta ce "Na sani" "To, kin san yaron nan da yayi suna a ƙofa, mai dogon zamani?" "Eh ina jin sunansa sosai" "To mariƙiyarsa, ƙawata ce tare muka yi boarding ai rahila shehu, kwana biyu bamu haɗu ba, kwatsam na je ƙofar na'isa na ga ɗan ta, ya rakani har gidan, to ita ma haka take fama da shi, ta rasa sukuni, kullum cikin tashin hankali take, neman maraba take da shi, uban ya kore shi, amma yaƙi barin gidan, kin ga idan aka aura mata shi, mun huta, a fake da fyaɗe aka yi mata, kuma dai ga tambarin da ki ka yi uwarta na maita, kawai dai ki lallaɓa maganar, kin san yadda zaki yi dai sabgar nan ta yiwu, wallahi muddin ba ta bar gidan nan ba, bana tunanin za a din ga kula namu, kuma wallahi ta auri mai kuɗi, kashinmu ya bushe, ai kin san riƙon da muka yi mata". Mama tayi ajiyar zuciya ta ce "Maganarki duka gaskiya ne, kar ki damu, wannan shawarar ta yi, kuma na aminta da ita, yadda muka kwashi baƙincikin uwatta, ita ma ba zata ji daɗi ba. Duk da wasu lokutan tana bani tausayi tana da biyayya, amma idan ba haka ba, namu ba zasu auru ga irin wanda muke so ba, ki gayawa ƙawartaki azo a nema masa aurenta, zan ji da komai" Anty ta washe baki ta ce "Alhamdilillah, magana ta ƙare". Jauhar kuwa, ba ta san me ake  ƙulla mata ba, ita lissafinta yadda za ta mayar da jarinta, dan tun da ta farka a asibiti, da ta dawo gida sai jakarta babu kuɗin cinikinta, dan ma mai shirin dutse ta yafe mata. Duk yadda take jin nauyin yin roƙo, haka ta cire kunya, ta tambayi yaya saifu ya taimaka mata da jari, ta cigaba da sana'arta, kuma cikin ikon Allah ya bata, saboda ta hannun daman sa ce sosai da sosai, aiki duk yawansa duk wahalarsa babu ƙyuya take yi masa, gyaran ɗaki, wanki guga idan baya nan tayi girki, ta zuba ta kai masa ɗakinsa, idan ya gama ci ya bar kwanukan a ɗakin, ta kwaso ta gyara masa, dan haka baya jin ƙyashin kyautata mata sam. *** Abbu yana daga kwance ya kammala azkar, ya juya zai yi bacci, rahila ta shigo ɗakin, ta nemi wuri ta zauna a kan gadon ta ce "Tun da idonka biyu tashi mu yi magana" Ya juyo ya ce "Ina jinki" "Magana ce mai muhimmanci, a kan Aminu". "Aminu dai Aminu dai, me kuma ya faru wannan karon?" "Menene ma bai faru ba, tun da an mutu an bar mini jaraba da masifa, kullum hankalina a tashe, nan aka zo ana bayar da labari, sun je ya tayar da tarzoma, har an yanke shi a ƙafa, rashin mutuncin sa kullum ƙara gaba yake yi" "To, na ji, maganar kenan ki sake maimaita mini abun da yake aikatawa? Wannan ai wani abu ne da na riga na sani". "Ba shi ne ba, magana ce a kan mafita game da abun da yake yi" Ya tashi zaune ya ce "Wace irin mafita?" Rahila ya gyara zama ta ce "Akwai wata ƴar ƙawata, yarinyar rashin ji take yi, tana neman fanɗarewa, gashi ba ta da wani tsayayye, na ce tun da shi gashi, kuma akwai wannan kangon gidan da ya gada, a gyara masa ka nema masa aurenta, ta je su ƙarata ko zai yi hankali idan ya ajiye iyali". Abbu ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Too, ikon Allah, banda abunki wane mai hankalin ne zai bawa Al'amin auren ƴar sa, yadda suanansa ya yi shuhura, a kan rashin ji". "To ai yarinyar na ce maka fitina take yi ita ma" "Kuma sai ayi gyaran ɓarna da ɓarna? Sai a aura masa wadda ba ta ji?" Rahila ta ce "To shi ɗin menene? Shi na kirkin ne?ko Jin yake yi? Sai su rufawa juna asiri, amma aka ƙyale shi a haka, nan da shekara ashirin, kana ganin zai yi nutsuwar da zai kula wata mace da sunan zai aura, tsabagin wauta da kayen maye ne kawai a cikin kansa" Abbu ya numfasa ya ce "Maganarki haka take, amma kamar yayi ƙanƙanta ma da auren shekara ashirin da bakwai, ga ba sana'a yake ba sai ɗaukar magana, da yaya zai riƙe auren? ga faɗa da faɗin rai". "Idan ya san ya ajiye mace, dole ya nemo ya ba ta ai, tun da morarta zai din ga yi, ko kuma kana tunanin zafin rai da faɗin ransa zai hana shi, mu'amala da ita ne namiji ne fa". Abbu yayi murmushi, har sai da haƙoransa suka fito, ya ce "Na san ɗa na kamar yunwar cikina, ban san meyasa mata ku ke tunanin maza, bamu da wani tunani idan ba wannan ba, Aishikenan". Ta kwanta ta ce "Aikuwa idan haka ne, da sai an dangana da nema masa magani, idan baya wannan tunanin" Ya kwanta a kusa da ita ya ce "Zuwa da safe in Allah ya kaimu, sai ki yi mini kwatancen gidan su yarinyar, na samu mahaifinta". Ta ce "Yauwwa Abbu ko kai fa" **** Jauhar ta dawo daga makarantar dare, ta tarar da Baba da baƙo a waje, ta durƙusa ta gaishe su, sannan ta shiga cikin gida. Baba ya nuna wa Abbu ita, ya gaya masa ita ce jauhar ɗin da suke maganarta, Abbu sam bai ga alamar rashin ji, a tare da jauhar ba sai ma nutsuwa da kamala, hatta muryarta mai sanyi ce, yayi mamakin da rahila ta ce masa wai ba ta ji, fanɗararriya ce, sai dai bai yi magana ba, suka cigaba da magana da Baba a kan nemawa Al'amin auren jauhar, ya sanar da baban jauhar Al'amin ɗin ba ya ji, sai dai bai gaya masa irin rashin jin ba, ya zata Baba ya san komai, saboda yadda rahila tayi masa bayani. Baba ya ce "Babu damuwa, Allah ya tabbatar musu da alkhairi, na san iyayen nata ba za su zaɓa mata abun da zai cutar da ita ba". Suka taɓa hira, ya tambayi Baba ko akwai wani shiri da za su yi? Baba ya ce idan sun shirya kawai su kawo abun da suke da shi, ayi komai a wuce wurin. Suka gama magana, Abbu ya tafi gida yana farinciki, tare da fatan Allah ya sa ƙarshen matsalar Al'amin ce ta zo, Shi ma Baba ya shiga gida, can ƙasan zuciyarsa yana ta kokwanto da wasi-wasi, amma ya kasa ayyana hakan a zahiri.Sam  bai iya tambayar menene rashin jin da  Aminu yake yi ba, bai tambayi menene sana'arsa ba da sauran su, kawai shi dai ya tsinci kansa da amincewa, bayan da mama tayi ta jaddada masa idan har Alhaji mu'azzam ya dawo, ya ji ƴan daba sun yi mata fyaɗe za ta wulaƙanta, ba zai aureta ba, shi gaba ɗaya ma ya manta da batun ya karɓi kuɗin auren Jauhar. Abbu na komawa, Rahila ta tare shi, tana tambayarsa yadda suka yi, ya ce "Ya amince zai ba shi ita, amma ni da ya nuna mini yarinyar, ba ta yi kalar marasa ji ba". "Ban da abunka Abbu, dama a goshi ake gane marasa jin? Kai dai kawai ayi sha'ani". "Amma anya ban yi ganganci ba kuwa, ban sanar da shi ba na je na nema masa aure, idan ya bujire fa". "Au sai ma ya yarda? Ashe na kabari zai dawo duniya idan shi ne zai yadda, ka yi iya yinka a matsayin ka na uba, kar ma ka sanar masa, sai ka kai kuɗin, kuma ku saka lokaci kaɗan, kar ya tafka wata tsiyar, ba akwai gidan da ya gada na wurin babarsa a chiranci ba, aje a ɗan gyara masa, ya zauna". Abbu ya jinjina kai ya ce "Shikenan Allah ya yi mana jagora". Kwana huɗu, Abbu ya kira baba, ya ce za su zo, su kawo dukiyar aure. Ko da Baba ya sanar da wanda za su karɓi kuɗin Jauhar ɗin tare, sun yi mamaki, suka din ga tambayar sa, meyafaru da waccan saka ranar, ya ce musu matsala aka samu. Dubu ɗari uku da hamsin, aka kai kuɗin komai da komai, har da lefe da sadaki da kuɗin aure, wai bayan sati biyu za a ɗaura aure. Mama ta fito tsakar gida ta din ga rangaɗa guɗa, suna Allah ya sa za su gani, gaba ɗaya sai jauhar ta zama confused, wane irin abu ne haka? Alhaji mu'azzam ne ya dawo? Ko kuma yaya aka yi, aka kuma karɓar wani kuɗin. ta ji ana zancen wani Al'amin shi kuma daga ina? Ta tambayi kanta. Sai dai tsananin kunya, da kawaicin jauhar, bai sanya ta yi magana ko ta tambaya ba. Su surayya suka din ga yi mata dariya, wai ta ga samu ta ga rashi, from grace to grass. Duk wani shirin auren, Mama ce take yi, ita ke karɓar kuɗin a hannun Baba wani abun ta saya mata mai kyau, wani akasin haka, masu kyan ma tana saya ne, saboda kar a yi mata gori, ta riƙe yarinya shekara goma sha shida za a shiga sha bakwai, amma ba ta yi mata abun kirki ba. Aminu kuwa tun kan a kai kuɗin, yayi ɓatan dabo, dan rigimarsa ba ta ciwo shi ya zo gidan ba, dan haka tilas Abbu ya fara bin dabar da yake zama, da duk in da ya san zai ganshi, amma babu shi babu labarin sa, haka ya din ga bayar da cigiyarsa, kamar wani kuɗi, kowa ya tambaya sai ya ce masa bai ganshi ba. Rahila ta ce masa ya cigaba da shirin sa, duk in da ya tafi ma zai dawo. A gidan su jauhar kuwa, hankalinta ne ya tashi, da ta ji Anty na yi mata iƙirarin wai nan da sati biyu za a ɗaura mata aure, da angonta Al'amin. Saifu ya kasa jurewa, ya samu Baba ya tambaye shi, wai meke faruwa da auren jauhar ne?. Baba ya ce "Eh, nan da sati biyu za ayi" "Amma na ga kamar sau biyu aka kawo kuɗin, wancan an ce Alhaji mu'azzam, yanzu kuma an ce Al'amin wanne ne gaskiyar lamarin ne?" Baba ya ce "Maman ka da Antynku, ne suka yanke shawarar a aura mata wani, wancan za a iya samun matsala, ta ɓangaren zakiyya ma aka kawo wannan ɗin" cike da takaici yake kallon Baba ya ce "wace irin matsala kuma Baba? Meyasa wanda aka kawo ɗin ba za a haɗa shi da wata ba, sai jauhar? A ina yake, kuma menene sana'rsa? Yazo ya ganta ta ganshi, yayi mata?" Baba ya sunkuyar da kai tare da girgizawa ya ce "No, amma na san ba za su zaɓi abun da zai cutar da ita ba, kuma jauhar yarinya ce mai biyayya" Takaici ya ishi Saifu, ya tsani yadda matan gidan suke shirya wa Baba abun da suke yayi, kuma yayi babu musu mussaman a kan jauhar. Kawai ya tashi ya fita tsakar gida, ya tarar da ita, tana ta uban wanke-wanke, gefe ta jiƙa kayan wankin uniform ɗin ƙanan yaran gidan. Ya ja kujera ya zauna a kusa da ita ya ce "Waliyiyya, wai saura sati biyu aurenki?" Tayi yaƙe ta ce "Haka na ji, amma dai Baba bai gaya mini ba". "Wanda zaki aura ɗin kin taɓa ganinsa ne? Ki na son sa?". Ta sunkuyar da kai tana murmushi ta ce "Ko ban ganshi ba, tun da an ce su mama ne suka zaɓa mini shi, kuma Baba ya amince na san ba zai cutar da ni ba" "Baki taɓa ganinsa ba kenan?" Sai ta kasa amsa masa, ta cigaba da durza tukunyar hannunta cikin ƙarfin hali. Can kuma ta ce "Dan Allah yaya, ka roƙi baba, ya ce masa dan Allah ina son ƙarasa makarantata, ko WAEC na yi" Saifu ya girgiza kai ya ce "Ki kwantar da hankalinki, na san juriya kawai ki ke yi, amma in sha Allah, ba zaki ji kunya ba jauhar". Mama ce ta fito ta ce "Kai saifu, uban me ka ke gaya mata, hure mata kunne zaka yi?" Ya tashi tsaye ya ce "Ko na hure mata kunne, ba zai huru ba, kawai ina tausayin sauran ƴan matan ne, saboda komai nisan jifa ƙasa zai dawo" Ta ce "Saifu ni ka ke gaya wa haka? Me ka ke nufi?" "Mama kin san fa me nake nufi sarai, Allah ya haramta zalunci a kan kansa, babu wanda zai yi ya tsira wallahi" ya ƙarasa maganar yana ficewa. Cike da takaici da son hucewa, mama ta rarumi takalmi, ta jefi jauhar da shi a fuska, aikuwa ya tsokane mata ido. Ta zauna ta din ga mutsutsuka idon, sai da idon yayi taruwar jini. Ƴan unguwar su jauhar sai ganin invitation suka yi na bikin jauhar, suka din ga zuwa gulma da jin ba'asi, wane irin aure ne haka faka-faka ko lefe ba a nuna musu ba, da yake ba su san ma zancen kawo kuɗin auren farko ba. Mama da zakiyya, suka din ga cewa saboda ayi a rufa mata asiri, ake son ayi gaggawa a aurar da ita, sadakarta aka bayar babu ko kayan lefe. Saboda cin fuska a gabanta, suke faɗar hakan. A gabansu sai ta jure, tayi kamar ba ta ji ba, idan ta ɓuya kuma sai tayi ta kuka. Al'amin kuwa, honorable Indabo ne ya saka aka kai shi asibiti ta ƙarfin tsiya, saboda ciwon ƙafarsa an sake fama masa lokacin da ya tayar da rigima a wurin campaign, a haka yake lanjarata, ya tafi nasa wuri, saboda soyake Aminun ya warware sosai, kafin lokacin zaɓe kuma, yadda zai yi masa aikinsa yadda yakamata. Yana shiga arearsu, aka sanar da shi cewa, babansa yana ta yawon nemansa, mamaki ya kama shi, dan idan zai kwana nawa bai ganshi ba, babu ruwansa da in da yake, dan haka cikin gaggawa ya nufi gidan, domin jin dalilin neman nasa. Sai dai da ya je ya tarar da Abbun yana shirin fita. "Kai baka iya sallama bane Al'amin, sai dai mutum ya ga ka bayyana kamar wani shaiɗani?" "To meye marbarsa da shaiɗanin?" Tayi maganar ƙasa-ƙasa. Sarai ya ji ta, amma ya yi shiru, ya samu wuri ya zauna ya miƙe ƙafarsa ya ce "An ce kana nema na" "Ba an ce bane, nemanka nake yi, ka dawo daga gantalin kenan? Kodaye ba yau ka fara ba, ka buɗe kunnenka da kyau ka saurare ni" Yayi shiru bai ce komai ba. "Daga nan ba kasuwa zani ba, Abba ne zai je ya buɗe shago, gidanka na chiranci, na gado zan je, za ayi masa wasu ƴan gyare-gyare, ba ni da kuɗi sosai a hannuna, za a yi masa abun da ya sauwwaƙa, kai ka ƙarasa gyarawa daga baya". Ya yi shiru yana wasa da zobensa, kamar yadda ya zame masa ɗabi'a, idan ba ya son yin magana. Abbu ya cigaba da cewa "Kuɗin aure na kai maka, next week za a ɗaura maka aure" Lanƙwashe ƙafarsa ɗaya yayi, ya koma wasa da yastun ƙafarsa, yana kallon wani wurin daban. Rahila ta ce "Taɓɗijan, lallai gagare". Abbu ya ce "Al'amin da kai nake fa" Ya ɗago idonsa ya kalli Abbu ya ce "Wai ni ko wa?" "A'a da ubanka nake ba kai ba, ni da waye a wurin nan?" Al'amin ya ce "Ni fa yau ban sha komai ba, garau nake balle ace a buge nake ban ji dai-dai ba, wannan kawai zance ne, ni da ake cewa gagarrare haihuwar asara, wa zai bani wani aure? Ni bana buƙata, idan kuma ba haka ba, duk abun da ya biyo baya ba ruwana idan na kashe yarinya, ko na yi mata illa, kar a zo ana yi mini ƙanan maganganu, ba na so bana buƙata". Ya yinƙura zai fice, Abbu ya riƙe shi ya ce "Umarni nake baka, ba shawararka ko ra'ayinka nake nema ba, dole ne wannan, aurenka wani satin, na kai kuɗin aure da komai, dole ka nutsu ka shiga hankalinka, idan ka illata musu ƴa ko kasheta kuma, zan sallamawa duniya kai, wannan shi ne hukuncin da na yanke" A fusace ya ce "Meyasa zaka yanke wa rayuwata hukunci, ba tare da amincewata ba bayan ka daɗe da sallamawa duniya rayuwar tawa? Ka yi hakan ne saboda farincikin matarka ko? Ta daina ganina na gusa na bar mata gidan nan ita da iyalinta. Da zan iya wallahi garin zan bar muku na ɓacewa ganinku ku samu cikakken kwanciyar hankali kamar yadda ku ke buƙata, amma ba zan iya ba. Ka sani ina ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, da gaske zan iya kashe ƴar mutane, ko na illata ta, sai dai ba na fatan na fi haka lalacewa, idan ka yi mini baki, zan ƙara lalacewa ne zan bi umarninka, amma duk abun da na yi mata da ni da kai zamu ɗauki nauyin zunubin. Saboda ni babu mata a tsarin rayuwata, miyagun halittu da babu Allah a ransu, bana fatan raɓar su, saboda yadda tasirin kaidinsu ya kassara rayuwata, kassarawar da ba za ta gyaru ba, mace ɗaya da nake wa kallon rayuwata, uwata kenan na rasata a yanzu babu wata mace mai sauran kima da mutunci a idona, nayi alƙawarin nesanta kaina da mata, nesantawa mai nisa ta har abada, amma ka karya mini alwashi, ta hanyar janyo mace rayuwata, ina sake nanata maka, duk abun da ya biyo baya, tare zamu ɗauki nauyin zunubin". Ya saka hannu, ya cire hannun Abbu da ya riƙe masa riga, ya saka kai ya fice. Har ya bar gidan, babu wanda ya sake magana, daga ita har Abbu. Gaba ɗaya aka hana jauhar fita daga gida, ana ta shirin biki, ita kuma tana rama kamar ana tsotseta, duk ta fiƙe sai farar fata da idanuwa. Maƙwabciyar su ta din ga cewa "Gaskiya mama ban so a aurar da jauhar yanzu ba, na so a bari maƙerin budurci ya gama ƙere mana ita, wannan kyawun da gidan wani hamshaƙin ya dace" Anty ta ce "Wannan ma hamshaƙin ne". A gida mama ta saka su surayya sa walida, suka dinga kwaɓe-kwaɓe suna murzawa jauhar da sunan gyaran jiki. Malam jamilu ya shiga matsananciyar damuwa, da samun labarin auren jauhar, dan har ga Allah yana matuƙar sonta, tsoron kar ta daina ganin mutuncinsa, ya sanya ya ɓoye mata. Gidan jauhar da aka je jere, yana da girma, sai dai tsakar gidan tsurar ƙasa ce, cikin ɗakuna babu floor, sai dai an yi plasta a ɗakunan, falo ɗaya da ɗakuna uku a ciki, kowanne da banɗaki, sai kitchen a tsakar gida da tsakar gida mai girma. An yi wearing ɗin wutar lantarki, a gidan. Sai buhunhuna, aka shimfiɗa a ƙasa, sannan cikin ɗakunan aka saka leda, falo kuma aka shimfiɗa carfet, saboda duk turɓaya ne. Tagogin duk babu na kirki, sai kame-kame da faci. Sai kujerunta, ƴan gida masu kyau, ɗaki ɗaya an saka furnitures, ɗaya kuma sai aka saka ƙatuwar katifa da wardrobe mai biyu, abun saka takalma. Duk da haka gidan ya yi kyau. Amarya ta din ga fargaba da tunanin, waye mijin nan, da haryanzu za ace, bai taɓa ganinta ba, kuma ba ta taɓa ganinsa ba? Kuma ya amince da zai aureta. Dogon gashinta baƙi, aka gyara mata shi, aka yi mata lalle ja da baƙi. Haka kurum take tuna Alhaji mu'azzam, a haɗuwarsu biyu, yadda yake nuna yana sonta, ba ta son ya zai ji ba, idan aka ce masa an yi mata aure. Kodayeke ita ba ta san dalilin fasawa da shi ba. Su liti suka lura da shirun Al'amin ya ƙara yawa, duk da ba mai yawan magana ba ne dama, sai ya zauna yayi shiru yana zancen zuci. Walid ya ce "Baaba, wai dan Allah kwanan nan meyake faruwa ne? Kamar ka na cikin damuwa" tabbas ba dan Walid ya tambaye shi yanzu ba, ba zai gaya masa ba. Ya karkace ya ɗaukko invitation a aljihunsa, ya miƙa wa walid. Wani irin ihu walid yayi, haɗi da kururwa, yayi katantanwa a ƙasa ya kuza uwar ashariya. Sannan ya ce "Allah dai ya biya maza, dama zaka afkawa sabgar nan, ka yi mana shiru haka? Ba ka gaya mana ba, balle mu shirya saura kwana uku fa". Sauran matasan da ke wurin suka miƙe suna tambayar Walid ko lafiya?. Ya miƙa musu invitation ɗin, take suka hau shewa suma, suna dara. Kawai ya dafe kansa, yayi shiru. Walid ya ce "Wai tsaya, auren dole za ayi maka ne? Na ga baka murna, kuma shi ne ba ka taɓa kai mu ehhh, mun gaisa da antyn namu ba, iya wuya mun samu mai dafa mana abinci" "Walid, Abbu ne ya shirya komai, ni ko ganinta ban taɓa yi ba, kuma ba na fatan na ganta, kuma ba kowa ne ya shirya wannan abun ba, sai wannan shaiɗaniyar matar ƴar haramun, ya ce umarni yake bani ba shawara ba, ni kuma na yanke guduwa zan yi, ba abun da zai haɗani rayuwa da wata mace, ba za a mayar da ni nusari ba, kalli yadda mace ta yi silar rushewar farincikin rayuwata gaba ɗaya" Walid ya zauna kusa da shi ya ce "A'a maza, duk lalacewar naka naka ne, kai ka san albarkar dattijan ke riƙe da mu, ka daina kallon abun da yake yi maka na rashin jin daɗi, idan yayi maka baki ƙara watsewa zaka yi. Duk da lokaci ya ƙure, dole ayi celebration, zamu gayyaci gayu a sha shayi a babbaka hayaƙi, abun farin ciki ya same mu" ya ƙarasa maganar suna shewa, ban da Al'amin da zuciyarsa kamar ta yi bindiga. Hatta kayan da Al'amin zai saka na aure, sai da Abbu ya saya wa Al'amin,  dan ko ganinsa bai sake yi ba, sai dai ya fita yawon neman sa. Ƙarfe goma na dare, su Walid suka shirya party, aka dafa shayi aka raba lemuka, da kayan shaye-shaye. Gogan yana gefe, yana zancen zuci, har ga Allah so yake ya gudu, amma ya san ya gudu alaƙarsa da Abbu za ta ƙara tsami. Kuma ya san ko ya gudu sai ya dawo, ba zai iya barin Abbun ba. Tunani yake kowace mai tsautsayin da ba a so, ce haka, aka zaɓi a aura masa oho. Ana tsaka da walimar hayaƙin, faɗan daba ya kaure, Al'amin kuma ya koma gefe ya ƙi magana, ƴan sanda suka yi wa wurin dirar mikiya, saboda rahoton da ƴan unguwar suka kai wa jami'an tsaro, ai kuwa suka kame su har da shi suka tafi da su ana gobe ɗaurin auren da bai san wacece matar ba. Ayshercool 08081012143 20 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Abbu kuwa hatta ɗinkin da Al'amin zai saka, ya yi masa, sai dai tun ranar da ya gaya masa, bai sake saka shi a idonsa ba. Yana zaune yana ta mitar rashin ganinsa rahila ta ce "Ba fa zama zaka yi ba, tashi zaka yi ka je ka nemo shi duk in da yake, kar ya kunyataka a idon duniya. Kana kallo yanzu na sauke mayafina daga gidansu amaryar, sun yi walima, duk sun gama shiri, na kai musu mukullin gida, har jere sun yi, fita zaka yi ka nemo shi ai" Haka Abbu ya shuri takalama ya bazama, aka sanar da shi, su na can wata unguwar, suna walimar aurensa. Ya bazama ya tafi, yana zuwa ya tarar da labarin ƴan sanda sun kama su duk sun tafi da su. Hankalin Abbu ya tashi, ya tafi division ɗin nan unguwar aka masa a station ɗin ma artabu aka yi da su, an kwashe su an kai su anti daba, ya ce wallahi ba za shi anti daba a daren nan ba saboda shi. Da ya koma gida kuwa, rahila kamar ta ari baki saboda mitar, meyasa bai je ba a sake shi, kar ya basu kunya, ya ce idan za ta iya, ta tafi. Jauhar kuwa su mama suka sakata a ɗaki, suna yi mata nasiha, fuskokinsu ɗauke da fara'a da jin daɗi, da nanata mata ba zasu zaɓa mata abun da zai cutar da ita ba. Ita dai ta damu sosai ta ga waye wannan mijin, da har suka ga ya dace da ita? Har a ranar idonta da kwanciyar jinin jifan da mama ta yi mata da takalmi. Washegari ranar juma'a, za a ɗaura aure a babban masallacin juma'a, amma Al'amin yana tsare. Sha ɗayan rana, sai ga P.A ɗin Honorable indabo a anti daba da kansa, ya je belin Al'amin, wanda ya yi hakan ne, saboda aikinsa da yake son ya ƙarasa masa. Suka din ga sara masa, suka gaisa ya gaya musu wurin wanda ya zo, yake son ya yi beli, da wanda ya aiko shi" "Gaskiya malam  yaron nan ba zai ci bulus ba, state CID zamu kai shi" P.Aya ce "Ayi haƙuri, in anjima za a ɗaura masa aure, ko dan albarkacin wannan a sake shi mana" "Wai ka san me ya yi kuwa?" "Eh, an ce sun yi shaye-shaye sun tayar da tarzoma ko?". "Ai da wannan ne da sauƙi, ya saba zuwa wurin nan a kan haka, jiya ƴan sandanmu sun kamo su, saboda sun sha tana gaya musu gaibu, a tsakiyar harabar station ya ɗaga ɗan sanda ya buga da ƙasa, saboda yana ganin ya isa, ya na ji da ƙarfi. Kuma ya din ga yi wa mutane wani shegen kallo kamar kumurci, zai gane kurensa, CID zamu kai shi" Ana haka shugaban kula da sashen ya shigo da shi da wani matashin ɗan sanda, suka ƙame suna sara masa, ya kalli P.A ya ce "Lafiya kuwa?". Suka gaisa sannan ya ce "Honorable ne dai ya kuma aikoni ayi ban baki, a saki Mai dogon zamani " "Ba su gaya maka laifin da yayi ba? Jami'inmu fa ya daka, ba ya ji yaron nan ko kaɗan" "Sun gaya mini, amma kamar yadda aka saba, honorable ya bayar da saƙo" Ya numfasa ya ce "A fito da shi da sauran yaran da ku ka kama" aka buɗe Al'amin, da yaransa, ya fito yana ɗan jirga ƙafarsa a hankali, saboda taron dangin da suka yi masa jiya, suka yi masa dukan tsiya, daga jami'in ya tankaɗa ƙeyarsa, ya waiwayo a fusace ya saka ƙafa ya kwashe shi a wurin. Daga shugaban, har PA ɗin babu wanda ya kalla, ya kama hanyar ficewa daga cikin station ɗin. Ya girgiza kai ya ce "VIPER kenan, Allah ya shirya". PA ya ce "Viper kuma?" "Eh sunansa kenan a gidan nan, sunan da suka saka masa kenan, ban san sau adadin da muka kama shi ba, ban taɓa ganin mutum mai bala'in taurin kansa ba, mu daka mu daka wallahi ko gezau ba ya yi, ga wani sheɗanin kallo da yake yi wa mutane, kai ka ce kumurci ne zai kai sara, shiyasa nake yi masa sha'awar hakar tsaro, yana da girma da kwarjini na gaske, amma shi ba a saka shi ba a hana shi". P.A yayi murmushi ya ce "Ai tun da ka ga honorable ya riƙe masa wuta, ba ya wasa da lamarin sa, kai ka san ba ƙaramin mara ji ba ne". "Eh ai ku ne ke goya musu baya" "Ai sabgar tamu ce dole sai da su". Kafin PA ya gama sallamar su ya fito, tuni su Viper sun ɓace. Har gida walid ya je ya sanar da Abbu, an sako su, amma yayi yayi da shi, ya taho gida yayi shirin ɗaurin auren yaƙi. Abbu ya bi walid, har in da Al'amin yake, ya mimmiƙe yana bacci, jikinsa duk shaidar dukan da ya sha a station. Maganar duniya Abbu yayi, amma yayi burus ya ƙi tashi, sai da ya cire takalmi ya hau ƙwala masa, sannan ya tashi da ƙyar yana muzurai, Abbu ya tasa shi a gaba zuwa gida. Ba ƙaramin kyau manyan kayan suka yi masa ba, yayi wani irin kyau na mussaman, kwarjinin da Allah ya yi masa ya fito sosai da sosai. Bayan sallar juma'a aka ɗaura masa aure, bayan an saukko daga masallaci, babu wanda ya sake ganinsa. Jauhar kuwa gabanta sai tsananta faɗuwa yake yi, ƴan ƙawayenta na makaranta, suna ta tsokanarta, suna yi mata raha, amma ta kasa sakewa. Mama ta hau ta da zagi a gaban mutane, wai sai ta saka an ce aure dole za ayi mata, taƙi walwala ko wanka ba ta yi ta shirya ba. Jiki babu ƙwari, jauhar ta yi wanka, aka yi mata kwalliya. Tayi kyau sosai da sosai, dama dai-dai gwargwado tana da hasken fata da kyanta na fulani. Baba ne ya fara dawowa gida, gaba ɗaya jikinsa a sanyaye, ana ta yi masa Allah ya sanya alkhairi. Ya saka aka kira masa jauhar, zuwa ɗakinsa. Cikin tsananin tashin hankali da damuwa, Saifu ya shigo gidan, yana ƙwalawa baba kira. Mama ta ce "Saifu lafiyarka ka ke yi wa mahaifinka irin wannan kiran haka?" Bai saurareta ba, ya shiga ɗakin baban, mama da anty suka bi bayansa, 'yan biki kuma suka yi cirko-cirko. "Baba wane irin miji ka aurawa jauhar? Tun a masallaci nake nemanka ban ganka ba" Baba yayi shiru, ya ƙi bashi amsa. "Baba magana nake yi fa kayi mini shiru yanzu zaka yi alfahari da wannan zaɓin da ka yi mata?marainiyar Allah, ka rasa wa zaka aura mata sai tantirin ɗan daba? Laifin me tayi maka har haka, mutumin arziki ya fito yana sonta, amma ka hana shi ka bawa mutumin banza, yanzu wane mutumin kirkin ne zai so haɗa zuriya da mai dogon zamani" A gigice jauhar ta ɗago idonta, gabanta ya shiga faɗuwa, tana jin yadda sunansa ya karaɗe arear unguwannin, duk da ba ta taɓa ganinsa ba, amma ya shahara da rigima da 'yan unguwar su, da shi da madaki tana jin sunayensu, ta san dai madaki, tun da cikin unguwar su yake. Cikin zafin rai saifu ya sake cewa "Baba ka yi mini bayani, menene dalilinka na yin haka?" "Saifu, kai ma ka fara shaye-shayen ne? Uban naka ka ke gaya wa haka? Shi ka ke tuhuma? Ba 'yar sa ba ce? Zai zaɓa mata abun da zai cutar da ita ne?" Ya ce "Zai yi mana mama, ke da wannan matar menene ba zaku iya aikatawa ba, kuma na san ku kuka ƙulla komai, akwai Allah" Jauhar kuwa kuka ta fara, amma ta kasa magana, jikinta ya din ga tsuma, Hafsa kuwa fita tayi, ta kira yaya tijjani, wai ga saifu can yana yi wa baba rashin kunya. Aikuwa ya shigo cikin gidan da sauri, zuwa ɗakin baba, sai faɗi in faɗa yake da mama, baba kuma ya ƙi magana. Yana zuwa ya ɗauke saifu da mari, sai dai yana sauke hannunsa shi ma ya rama, take dambe ya kaure, sai dai jin hayaniya a waje ne, ya sanya suka yi saroro. Bushe-bushen 'yan tauri ne yake tashi daga ƙofar gidan, nan da nan warin wiwi ya din ga shigowa gidan, yaran Aminu sun cika layin, suka din ga busar 'yan tauri, suna yi wa Aminu kirari, sai dai babu shi a wurin. Su maman ma waje suka yi, domin zuwa su ga abun da yake faruwa. Nan 'yan biki suka dare, wasu kuma suka tafi kallo. Baba ya riƙo hannun jauhar, da take ta uban kuka, kamar shi ma zai fashe da kuka ya ce "Fatima, na yi miki laifi, ban san yaya aka yi wasu abubuwan suka faru ba, dan Allah ki yafe mini, in sha Allah ba zaki wulaƙanta ba, zaki yi alfahari da hakan, na san na daɗe ina zaluntar rayuwarki, ina cutar da ke, dan Allah ki yafewa baba jauhar, kar ki yi fushi da ni, in sha Allah sai auren nan ya zame miki alkhairi" Ta share hawayenta ta jinjina masa kai ta ce "In sha Allah Baba" "Yauwwa yarinyar kirki, Allah ya yi miki albarka ya kare ki daga dukkanin sharri da abun ƙi, Allah ya kula mini da ke a duk in da ki ke.Na san dama ke mai haƙuri ce, zaki ci riba in sha Allah" ta jinjina masa kai tana ƙoƙarin haɗiye kukan da yake ƙoƙarin ciwota. Ba a rabu da bukar ba an haifi habu, ta san wannan auren wani sabon ƙalubalen ne a rayuwarta. Ƙawayenta tuni suka gudu gida, 'yan biki ma duk sun watse, ta samu wuri ta ƙule a ɗakinta, ta din ga kuka, tana neman agajin Ubangiji. Kwatsam! Yaran madaki suma suka taho layin, da niyyar tarwatsa yaran Aminu, dan kuwa ba sa jituwar da za su bari su shigo musu layi, su yi musu wannan budurin. Ba a jiyo komai, sai karafkiyar makamai, da zage-zage tamkar ana yaƙi. Suna daga cikin gidan, suka jiyo ana cewa tun da aka aurar da ƴar gidan ga maƙiyinsu, idan ta bar unguwar ta bar ta kenan, idan suka kuma ganin ta, sai sun sassarata. Mama ta ce "Zakiyya, kin ga wata tijara, ni fa hankalina ya tashi, ji kamar ana yaƙi". "To ke ina ruwanki, da an kaita ba shikenan ba, can su je su ƙarata ba" Suna cikin maganar, sai ga gwangwanin tiya gas, a tsakiyar cikin gidan ƴan sanda sun sake dira, su tarwatsa su. Jauhar ta ƙara takurewa tana kuka, saboda tsananin tsoro da tashin hankali, dan a kunnenta ta ji ana cewa, idan aka ƙara ganinta a unguwar ma, sai an sassarata. Unguwar ba ta yi dai-dai ba, sai bayan sallar la'asar, hatta sallar la'asar a gida aka yi ta a unguwar, saboda tashin hankali. Bayan Baba ya yi sallar la'asar, ya kira mama ya ce, ya shirya masa jauhar, ya kaita da kansa, tun kan yaran nan marasa ji su ce za su yi mata illa. Idanun jauhar duk sun kumbura, sun jawur saboda azabar kukan da ta sha. Mama tana dariya take cewa "Haba Jauhar, kowa da haka yake kafa nasa iyalin, da haka kowa ya saba" Jauhar ta kalli mama, iya wannan tashin hankalin bai isa ya sanya su gane sun jefa rayuwarta a garari ba, amma take yi mata wannan surutan? Haka ta yi alwala ta yi sallar la'asar, sai dai ta kasa addu'a ma. Ko kaya ba ta canza ba, mama ta ɗaukko mayafi, ta ce tare za su kaita ɗakin miji. Sun fito waje, Saifu ya kawo kai, yayi turus ya ce "Baba, yanzu wannan tashin hankalin da aka yi a unguwar nan, duk a kan auren nan, bai sanya ka saduda ba, ka haƙura? Baba ya yi masa shiru, ya yi gaba hannunsa riƙe da na jauhar, ya buɗe mata mota ta shiga baya, suka ja suka tafi. A can suka tarar da wasu daga danginsu Al'amin, a gidan suka din ga rangaɗa guɗa, da aka ce an kawo amarya, dan sun baro can gidan su Al'amin, a kan Abbu zai aika da motocin ɗaukko amarya, sai dai suna ganin Baba suka nutsu suka yi shiru. Har kan gado ya kaita ya zaunar da ita, ya riƙe hannunta, ya din ga yi mata addu'a, sannan ya sunkuya ya yi ƙasa da murya ya din ga yi mata nasiha, yana yi tana kuka, sai da ya gama ya din ga saka mata albarka ya ce mama ta wuce su tafi. Angon kuwa yana can dabar su, ban da bushe-bushen sigari, babu abun da yake yi, hatta dambarwar da aka yi a gidan su amaryar bai sani ba, shi dai ya san Walid ya ce za su gayyato 'yan gangi da 'yan tauri, ayi nishaɗi. Bai ma san a ina aka ya ba, balle ya san abun da ya faru. Sai wajen ƙarfe takwas na dare, Walid ya dawo, ya din ga ba shi labarin, abubuwan da suka faru, da yadda suka yi da 'yan sanda. A ƙalla ya kai mintuna goma sha biyar yana zuba, yana bawa Al'amin labari, amma bai tanka ba. Ya gaji ya ce "Maza, ka tashi mu shirya, mu raka ka gidan amarya". Sai a yanzu ya ɗago ya kalleshi, amma ya yi tsaki ya koma ya kashingiɗa. Walid ya ce "Wallahi ba ka isa ba, wai so ka ke sai Abbu ya yi fushi da kai? Dama na haɗa maka kayanka jiya, yau sai ka bar gidan nan, kai Allah ya ɗaga darajar ka, kana wasa da damar ka" walid ya cigaba da mita, yana ƙara haɗawa Al'amin kayansa a ghana must go, da masu dauɗa, da wankakku, har da takalma da brush, haka ya din ga danna su. 'yan uwan su Al'amin, babu yadda ba su yi ba, su ga fuskarta, amma fafur ta ƙi, ta din ga ƙudundunewa, suna nan tare da ita har tara na dare, suka gaji ga dare, masu zuwa ganin gida, duk suka gama, suka din ga tafiya, har ya rage saura itakaɗai aka bari. Nan hankalinta ya fara tashi, daga ita sai farar fitila mai batir, tana ta addu'a a cikin zuciyarta cike da fargaba da tsoro. Tana ta tunanin kar 'yan daba su lallaɓo su zo su kasheta. Ta gaji da zaman wuri ɗaya, ta ga ledar pure water, a ajiye a falo, da 'yan ganin gida suka zo da ita, ta ɗauka ta yi alwala, ta yi sallolin da suke kanta, ta zauna zaman dirshen tana tuna ƙalubalen rayuwa da ta haɗu da su kashi-kashi yanzu kuma ga ta kuma a wani mataki, mai hatsarin gaske. Har bayan sha ɗayan dare, sai itakaɗai a gidan. Fargaba da tsoron da take ciki, ya ninku a zuciyarta. Kasancewar bacci ɓarawo ne, haka ya yi awon gaba da ita daga nan in da take a zaune kusa da gado. Sai dai ba ta san adadin lokacin da ta shafe tana baccin ba, ta farka a razane, taga hasken wutar lantarki an kawo wuta. Ji ta yi kamar motsi a falon, ta lallaɓa ta leƙa cikin tsoro da tashin hankali bakinta ɗauke da addu'a. Wani dogon mutum ta gani a kwance a kan doguwar kujera, ya juya bayansa, ya duƙunƙune da babbar riga, da alama sauro ne ya dame shi, ya lulluɓa. Gabanta ya faɗi, ta koma ta zauna tana tunanin, wannan shi ne angon ko kuwa? Iya ƙoƙarinta ta dage kar ta kuma komawa bacci, saboda tsoron da take ciki. Al'amin kuwa, Walid ne ya taso shi a gaba, ya kai shi har gidan, daga shi sai shi, da ƙullin kayansa a ghana must go wajen sha ɗaya da rabi na dare. Suna tafe yana lallaɓa shi, sai da ya tabbatar ya shiga, sannan ya tafi. Ya shiga yana ƙarewa gidan kallo, shi dai ya san gidan kango ne, amma yadda aka jera masa kaya, yayi kyau. Yana shiga falon, bai bi ta kan ina amaryar take ba, ya tuntsurar da ƙullin kayansa ya haye kujera ya mimmiƙe kamar gawar sababi. An fara kiraye-kirayen sallar asuba, ta shiga banɗakin cikin ɗakin, tayi alwala ta din ga nafilfili, har aka yi sallar asuba. Bayan ta idar tana cikin azkar, wani irin nannauyan bacci, ya kwashe ta a wurin. Sai da gari ya yi haske, sannan ta farka, ta tashi tana salati, ta tashi tana ƙarewa ɗakin kallo. Yayi kyau sosai da sosai, duk ko fenti babu amma furnitures ɗin sun yi kyau. Ta fita falon gabanta na faɗuwa, domin gaida mai gidan da no nemanta bai yi ba, sai dai ba ta gan shi ba, ta leƙa ɗaya ɗakin, amma baya nan, sai ghana must go a falo. Ta fito tana ta lelleƙa gidan, abun ya burgeta, duk da ba ƙerarren gida bane, amma ta ji daɗin cewar gidanta ne ita ke da iko da shi, amma da ta tuna haryanzu ba ta yi ido huɗu da angon ba, sai gabanta ya faɗi, ta fara tunanin ko shi ma auren dolen aka yi masa da ita. Tunawa ta yi, da 'yan dabar Unguwar su, sun ce idan suka kuma ganinta a unguwar su, sai sun sassarata. Gaba ɗaya ranta ya ƙara dugunzuma. Ta zauna shiru a falo, tana ta jira, ko wani zai zo mata daga gida, amma shiru babu wanda ta gani, ga yunwa tana ji, dan wunin jiya ba abun da ta ci, gashi ta kwana ta wayi gari ba ta saka komai a cikinta ba. Can kuwa, Rahila kuwa kamar ta taka rawa, ta rabu da ƙaya, Aminu ya bar mata gida, ta ƙara sakewa da ita da yaranta yadda take so, fargabar ta zata ragu sosai da sosai, ta san yanzu dole zai tattara ya bar unguwar ya ƙara gaba. Dangin mahaifiyar Aminu da suka zo, daga can ƙauyen tofa, ta din ga wulaƙanta su, dan sai da ta yi wa Abbu masifar dan me za a gayyato su, sai dai a hakan gudunmuwar dubu ɗari biyu suka bawa Abbu na auren. Ban da uban kayan abinci da suka taho da shi, suka ce a ƙara a kan na biki. Sai dai har suka yi kwana biyun, ko sau ɗaya ba su ga Al'amin ba, sai kwasar takaicin rahila, yadda take wulaƙanta su, tare da aibata shi, tana an mutu an bar mata riƙon masifa da tsiya. Washegari da safe, waɗanda ba su je ganin gidan ba, suka ce za su je su ga gidansa, daga nan za su wuce su koma tofa. Da Abbu suka yi sallama, Rahila kuwa ko kallo ba su isheta ba. Har wajen sha ɗaya da rabi na safe, jauhar na zaune na rarraba ido,  ta ji sallma a tsakar gidan. Amsawa tayi, tana jiran ƙarasowar masu sallamar. Mata ne wasu 'yan dattijai, da matasan 'yan mata. Jauhar ta karɓe su hannu bibbiyu, suka shigo falon suka zazzauna, hannunsu da kaya. Suka gaisa da jauhar, ɗaya daga cikinsu ta ce "Tubarkallah, Aminullahi ya mori 'yar kyakykyawar yarinya Tubarkallah, ya sunanki?" Jin abun da suka ce, ya sanya ta gane 'yan uwansa ne, ta ce "Jauhar" Suka din ga maimaita sunan nata, suna cewa sunanta na 'yan birni. "Ina Aminullahin ne? Tun da mu ka zo, bamu ganshi ba, gashi daga nan can gida zamu koma" cewat wata dattijuwar. Jauhar ta ce "Ya fita" "Ohh, ji soko, daga kawo masa amaryar jiya, har ya saka ƙafa ya fice, to Allah ya kyauta. Kin ganni ni kakarsa ce, ga yayar gyatuma tasa, nan duk 'yan uwan mahaifiyarsa ne, amma ba ya zuwa in da muke. Dan Allah kya ɗan din ga saita shi a hanya, ki yi ta haƙuri kin ji, Allah ya baku zaman lafiya" Kunya ta saka jauhar kasa amsa musu. Suka yi ta yi mata hira, amma ta kasa amsa musu, saboda nauyinsu da ta din ga ji, sai dai kakartasa mace ce mai barkwanci, suka ba ta kayan da suka zo da su, su tsintsiyar laushi da ta kwakwa, kaskon turaren wuta, kayan miya har da kuɗi. Jauhar ta yi tayi musu godiya, sai dai ranta duk babu daɗi, ga baƙi amma babu abun da za ta basu. Zuwa azahar, suka yi mata sallama suka tafi. Har la'asar babu wanda ya sake zuwa, ta ji babu daɗi sosai, rashin ganin wani daga gidansu ko mutum ɗaya. Yaran maƙwabta suka ɗan shisshigo mata, shigowar ta su tayi mata daɗi, ta basu kuɗi, ta ce su sayo musu buredi. Suka sayo, suka zauna, suka ci tare da su, ta ajiye wani da niyyar idan mai gidan ya zo ta bashi. Mama kuwa bayan sun koma gida daga kai jauhar, duk 'yan biki sun watse, kowa tayi ta kanta. Suka ƙule a ɗaki ita da zakiyya ta ce "Zakiyya duk da gidan yarinyar nan babu gyara, amma yayi kyau sosai da sosai" "Eh ai hakan yayi, ma rage wani surutun, har ku ka taho kuwa kun ganshi ya je gidan shi angon?" Mama ta ce "Ina fa, itakaɗai muka baro, sai wasu 'yan uwan babarsa, su ma na san ba zasu jima ba zasu tafi ba. Nifa sunansa kawai nake ji, ban taɓa ganin sa ba". "Zaki ganshi ne, ba dai ya zama sirikinku ba? Ni na san shi, amma lokacin yana yaro, ai kin san daga baya suka dawo ƙofar na'isa da ba a nan suke ba, ni tsoro nake ji ma kar yaran nan su cigaba da kawo mana farmaki" Mama ta ce "Babu abun da za su dawo su yi mana, mun yada ƙwallon mangwaro mun huta da ƙuda, yanzu menene abun yi?" "Abun yi, shi ne mu jira dawowar wannan Alhajin, mu ga yadda za a ɓullowa lamarin ya haƙura gaba ɗaya da batun ta" "Haka ne, to Allah ya dawo da shi lafiya, sai ayi ta ta ƙare, jauhar dai an aurar da ita, sai mu jira mu ga yaya zai kasance da namu 'ya'yan. Gidan jauhar magariba na yi, yara suka watse suka bar ta itakaɗai kamar tsohuwar mayya. Sai fitila ta kunna, ta saka mayafinta ta din ga korra sauro daga ɗakunan, saboda yadda suke ambaliya kamar a barikin su. Ta rurrufe ko ina, tana jiran ta ga ta ina ango zai shigo, amma shiru. Har bacci ya kuma cin ƙarfinta ya kwashe ta. Wunin ranar kuwa, Al'amin zarya ya din ga yi, sai da aka sakar masa yaransa da aka kama a unguwar su madaki, har suka sanar masa iƙrarin da 'yan unguwar da suka yi, na idan suka kuma ganinta a unguwar sai sun sassarata. A ransa ya ce Allah ya ƙara, maganinsu kenan, da suka ga babu wanda ya dace su bawa 'yar su sai shi. Tare da su ya wuni yana shaye-shaye, Walid ya na son ya yi masa magana, amma ya san yana yi za su yi faɗa, dan haka sai dare ya sake lallaɓa shi, daga can unguwar ya goya shi a babur ya kai shi gidansa na ɗorayi chiranci. Sai dai kamar jiya, kafin gari ya yi haske, ya sake barin gidan, gashi ko brush ba ta da shi, ba ta da kayan girki, haka ta kuskure baki ta cinye biredin jiya, gashi ba ta son cigaba da taɓa kuɗin da aka bata, yakamata ta nuna masa kayan da aka bata, saboda 'yan uwan sa ne suka bata. Ta fito tsakar gida ta samu wani ɗan tudu ta zauna, tana tunanin yanzu haka za ta rayu, wanda ya ajiye ta baya ko ƙaunar ganinta, kwana na biyu kenan haryanzu ba ta ga kalarsa ba ma. Tana son yin wanka da sauran buƙatu, amma ba hali, babu ruwa, ga rijiya a gidan amma babu guga, babu sauran kayan masarufi. Ƙwanƙwasa ƙofar da ake yi ya dawo da ita hayyacinta, ta tashi ta ɗaukko mayafi ta saka, ta buɗe a hankali. Saifu ta gani a tsaye, hannunsa riƙe da kaya. Ta washe baki ta ce "Yaya saifu" yayi murmushi ya ce "Na'am Waliyiyya" Ta bashi hanya ta ce ya shigo, ta karɓi kayan hannunsa, suka shiga har falo. Ya kalleta ya ce "Yaya babu wata matsala dai ko?" Ta girgiza kai ta ce "Babu" "Ina mijin naki yake?" "Baya nan, ya su baba? Ya su mama?" "Suna nan ƙalau, gida yaƙi kyau ba kya nan, duk 'yan matan nan an rasa wadda za ta yi aikin da ki ke yi" tayi shiru tana murmushi. "Ga sauran kayanki na kawo miki, na harhaɗo da na ɗakinki duk na kawo miki, muddin ki ga ya yi miki wani abu da baki gamsu ba, ki gudo gida kin ji ko?" Ta jinjina masa kai alamar to. Ya ce "Kina buƙatar wani abun ne?" Ta ce "A'a" Ya miƙe ya ce "Na san ba zaki faɗa ba ai" ya shiga kitchen ɗin ta yana dubawa, babu alamar an dafa wani abu. Ya ɗauki gas ɗin ta, ya fita da shi, ya yo mata refilling, ya yi mata sayayyar kayan shayi da 'yan kayan abinci, ya dawo ya kawo mata. Ya ce "Ki yi haƙuri jauhar, bani da kuɗi, amma zan sake dawowa in sha Allah, kar ki yadda da wani haƙuri, na san zaman aure haƙuri ne, amma kar ki zauna ana zaluntarki, ko ya ce zai dake ki, zan sake dawowa in sha Allah kin ji ko" ta ɗaga masa kai alamar eh, ya sayo mata guga, ya janyo mata ruwa ya tara mata, ta din ga yi masa godiya suka yi sallama. Bayan tafiyar sa, tayi wanka ta canza kaya, yaran maƙwabtanta da suka shgo, ta dafa musu taliya, suka ci ba ta gaza ba, ta ɗebarwa maigidan nasa ta ajiye. Sai dai yaran da wuri suka tafi yau, ta samu wuri tana wanke-wanke, ta ji kamar an wuce ta bayanta. Tashi ta yi a firgice, tana addu'a da tunanin ko gane-gane ta fara yi. Sai dai ta ga takalmi a ƙofar falon, kasancewar gidan akwai gate, kuma akwai ƙaramar ƙofa, ƙofar a buɗe take. Ta lallaɓa ta leƙa, ba ta ga kowa ba, ta shiga falon tana tambayar waye?. Fitowa ya yi daga ɗaya ɗakin, hannunsa riƙe da baƙar leda, kallo ɗaya ta yi masa ta gane shi, ƙwala ihu ta yi, ta ruga da gudu ɗakin da gadonta yake, ta rufe ƙofar ɗakin. Ayshercool 08081012143 21 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Hanyar da ta bi ya bi da kallo, yana tunanin a ina ya taɓa ganin fuskarta. A ransa ya ce "Mahaukaciya ce kenan, Shiyasa aka aura mini ita, haukana ya fi naki" ya fito daga falon ya saka takalmansa ya fice. Jauhar kuwa durƙushewa tayi, ta ɗora hannunta a ka ta ce "Na shiga uku" a take ta fashe da kuka ta ce "Allah ka sanya mafarki ne ba gaske ba, Allah ka sa ba wannan ne mijin nawa ba? A gabana ya kashe wani, Allah Ubangiji ka rufa mini asiri ka dube ni, ya Allah ka dubi maraicina da ƙangin da na baro, ka sassauta mini a nan, ya Allah ka sa ba shi ne mijina ba". Ta cigaba da addu'ar tana kuka, ta kasa fitowa sai ma ƙara sakata da ta yi a ɗakin tana kuka. A take komai ya dawo mata fes, yadda ta ganshi, ya yi kisan kai, hannunsa riƙe da mutum da wuƙa a gefen cikinsa. "Na shiga uku, ko biyoni yayi ya kasheni, me na yi masa wallahi ban gayawa kowa yayi kisa ba" tayi maganar ƙasa-ƙasa tana kuka. Ko da wasa ba ta yi yinƙurin, sake buɗe ƙofar nan, a banɗakik nan tayi alwalar magariba da ta isha'i, ta kasa addu'a komai, sai fatan Allah ya sa ba wannan ne mijinta ba. Ba ta sake fitowa ba, har garin Allah ya waye. Zaman ɗakin ya isheta, fitowa kuma ta gagareta, sai da ta leƙa ta ga babu kowa a falon, bakinta ɗauke da addu'a ta fito. Ba kowa, ta leƙa tsakar gida, ya rufe mata ƙofar, babu taklmansa kuma a wurin. Ta dawo falon, ya cinye taliya da man da da ta zuba masa tas, ya ajiye komai a wurin, hatta wadda ta ɗan zube a ƙasa bai kwashe ba, jug ɗin ma daban kofin jug ɗin daban. Ta kwashe komai ta fitar tsakar gida, ga sauran kwanukan da ta fara wankewa ta bar su a wurin, komai yana nan. Sai zuciyarta ta fara raya mata, ai ba shi ne mijin nata ba, ya shigo ne kawai ya tsorata ta, sai ta cigaba da addu'a Allah ya ƙara nesanta ta da shi. Ta yi 'yan gyare-gyaren ta na gida, yaran da suke shigo mata, yau ba kowa duk sun tafi makaranta, ga tsakar gidan wasu irin manyan ƙadangaru suna bin bango, dan haka fitowa tsakar gidanma wahala yake bata, saboda tsoro. Ta datse gidan, yadda babu wanda zai shigo sai ya bubbuga. A jere ta sake jera kwana biyu ba ta sake saka shi a idonta ba, akwai ranar da bai kwana a gidan ba. Bai sake dawowa da rana ba, sai cikin daren nan, idan ya tarar da abinci ya zauna ya cinye abun sa, kafin ta tashi ya fice. Abun ya fara damunta, ga tsoron gidan take ji, sosai da sosai. Wajen la'asar ta ji ana buga ƙofa, ta din ga tambayar waye, amma ta ji shiru. Har zata haƙura da buɗe ƙofar, ta zata ba kowa, aka kuma buga gate ɗin maimakon ƙofar da ƙarfin gaske. A tsorace ta buɗe, aikuwa ya hankaɗo ƙofar, ta kuma kurma ihu, ta kwasa da gudu, ta shiga kitchen ta rufe ƙofa. Sororo ya tsaya yana tunanin, ihun me take yi dan ta ganshi? Ya basar ya shiga ya yi abun da zai yi ya fice. Sai a yanzu ta fara gazgata lallai wannan ne mai gidan, shi ne mijin da aka aura mata. Cikin kuka ta ce "Allah komai ka yi dai-dai ne, Allah ka sanya shi ne mafi alkhairin da nake ta fata". Ta sanya wa zuciyarta za ta yi ƙoƙarin, danne tsoronsa da take ji, amma abun da ba ta gane na shi ne, ba iya abun da ya faru waccan ranar ne kawai yake ba ta tsoro ba, tsananin kwarjinin sa ne ke ƙara rikita ta. Suna dabarsu, Al'amin yana ta shan sigari, Walid ya ce "Maza, gaskiya abun da ka ke yi baya dacewa, an kai maka mata, amma kullum kana nan kana cakewa, akwai matsala ne?". Al'amin ya rausayar da kai ya ce "Yarinyar Mahaukaciya ce ashe" Cikin rashin fahimta ya ce "Mahaukaciya kamar yaya?". "Kamar yadda na gaya maka, ihu take yi itakaɗai" Walid ya ce "Ko dai tsorata ta ka ke yi? Ki tsaya kun yi magana kun gaisa?" Aminu ya ce "Da wa?" "Da amaryar mana" ya ja tsaki, yana mayar da sigari bakinsa. "Wallahi Aminu da ni aka yi wa auren gatan da aka yi maka da na more, haba baka kyautawa gaskiya " Yayi masa shiru, yaƙi ko kallonsa, dan ko zancen auren ba ya son ji, haka kurum ji yake yi kamar an yi masa dabaibayi. Saifu kuwa yanzu ban da gaisuwa, babu abin da yake haɗa shi da da mama da Baba, dama Babar su hafsa Zakkyya ba shiri suke yi ba, ko kallo ba ta ishe shi ba. Sai dai sun fara zancen a kawo 'yar aiki, dan duk yawan 'yan matan gidan nan, ba sa iya aikin gidan, girki sai dai a jagwalgwala, wani ya ciwu wani ba zai ciwu ba, gidan nan kuwa wasu lokutan kamar fadar mahaukaciya, dama jauhar ce ana ɓatawa tana gyarawa, yara na cire kaya suna zubarwa tana kwashewa, amma yanzu bata nan babu mai gyarawa. Baba kuwa ƙasan zuciyarsa yana nadamar auren da ya yi wa jauhar, amma ba zai iya nuna hakan ba, ya duƙufa yana yi mata addu'ar samun kwanciyar hankali a gidan aurenta. Cikin dare da ya dawo, ya ji gidan a rufe, bai tsaya jiran komai ba, ya kama katanga ya dira kamar ɓarawo. Gaba ɗaya jauhar a zatonta, itakaɗai ta kwana a gidan, saboda ba ta ji bugun ƙofa ba, ta fito tana ta share-sharenta, ta ɗora ruwan zafin dafa makaroni, saboda su yaya saifu ya sayo mata, taliya makaroni, mai maggi sugar da sauransu. Ta fara bin ɗakunan tana gyarawa. Sai dai ta din ga jin warin taba, ta rasa daga ina take jin warin. Kawai ta nufi ɗakin da yake ciki, ba tare da ta san yana ciki ba, ta afka, a zatonta ita kaɗaice a gidan. Yana kashingiɗe yana zaune yana kaɗa ƙafa yana shan tabarsa, ya zazzage kayansa a kan katifar ɗakin, ghana must go ɗin, ya cillar da ita a tsakar ɗakin. Har da takalma a kan katifar, soson wanka da brush duk suna kan katifar. Ba wannan ba kawai, har da ledoji da kwalayen taba, ga tokar maganin sauro ko ina. Kamar mahaukaciya haka ta juya, ta ɗiba da gudu, sai dai a wannan karon, rufa mata baya ya yi, ya cimmata, tana ƙoƙarin rufe ƙofar ɗakin da ta shiga, ya hankaɗa ƙofar ta faɗi jikinta na wata irin tsuma. Ya zuba mata ido, wanda ya haddasa mata tsuma da karkarwa cikin razani da matsanancin tsoro. Bai ce mata komai ba, sai cigaba da kallonta da yake yi. "Dan Allah ka yi haƙuri, wallahi ban gayawa kowa ka kashe shi ba, dan Allah ka yi haƙuri, ni matar aure ce, ka daina shigo mini gida" tayi maganar wani irin gumi na tsatstsafowa daga fuskarta. Ya sunkuyo saitinta, warin sigarin da ya sha, tana dukan hancinta, sai a lokacin ya gane ta, ya gene a in da ya taɓa ganinta. "Kin ganni na kashe shi?" Ta jinjina kai alamar eh. "Mahaukaciya ce ke? Ki na da taɓun hankali ne?" Ta girgiza masa kai alamar a'a, tana ja da baya. "Idan ki ka kuma ganina, ki ka gudu kina ihu" ya zaro wuƙa a ƙugunsa, ya nuna mata. Sannan ya ce "Sai na yi miki abun da ki ka ga na yi wa wancan mutumin, wato in kashe ki" Ta girgiza kai ta ce "In sha Allah ba zan sake ba" ya miƙe, ya mayar da wuƙarsa ya fita ya bar ta. Wani irin numfashi ta din ga saukewa, cike da tsoro, ta ƙara gazgata cewar, shi ɗin ne dai mijinta ba wani ba. Ta jima a wurin tana kuka, sannan ta tashi a hankali, ta sake komawa ɗakin da ta gano shi. Ɗakin yana nan, kamar mahaukaciya ta buɗe dealer, ya watsar da komai, sai warin sigari ɗakin yake yi. Ta ɗaɗɗaga labulaye, ta zo ta durƙusa ta fara ware kayansa, wankakku da masu datti, ta kwashe takalmansa, ta jera masa a bayan ƙofa, wankakkun kayansa, ta shirya su a cikin wardrobe, marasa wankin ta fita da su, ta share ɗakin tsaf, ta ɗauki brush ɗin sa da toothpaste, ta kai masa banɗakin cikin ɗakin, da bokiti da buta. Kayanta akwai turarukan wuta, da aka bata na gudunmuwa, sai dai ba ta da gawayi, dan haka ta kunna na tsinke, ta sassaka a ko ina, saboda korar warin sigarin nan. A cikin kayan sa ta ga wata Mp, ta ɗauki mp ta kunna ta ji tana yi, ta kunna radion jiki, ta ji tana yi, ta fita tsakar gida da ita, tana ta aikace-aikace, da zummar kan ya dawo ta kashe ta ajiye masa, ta ɗan ɗebe mata kewa, ta manta ko sallama baya yi kafin ya bayyana. Gidan su jauhar, akwai maƙwabciyar su Anty lubabatu, tana tausayinta sosai, suna mutunci da juahar, dan idan ta haihu, jauhar ta yi ta zuwa gidanta, dan ta ɗauki yaranta, ita ce ta haɗata da 'yan gidan su, take karɓar shirin dutse tana yi. Tun washegarin kai jauhar, ta shiga gidan ta ce wa su mama, a bata mutum ɗaya ya rakata gidan jauhar, amma suka ce ba wanda ma ya san gidan. Jauhar kuwa, ta gama aikinta tayi wanka, gidan babu komai na abinci, sai taliyar nan da macaroni da yaya saifu ya saya mata, gashi sun isheta, sai dai babban abun da yake yi mata daɗi, tana da damar ta dafa ta ci yadda take so, saɓanin idan a gida ta girka, sai ta gama wahalar a sanmata. Tunani take yi, idan ta dafa taliya yau ma ko zai ci, tana tunanin ko shi ma sun fara isar shi. "Karfa ya ce ko ban iya girki bane, shiyasa kullum nake dafa taliya. To ai gidan bakomai sai su" Ta ɗan yi shiru, tana tunanin yau bari ta aika a sayo mata kayan miya, tayi da miya, so take ma ta nuna masa kuɗin da kakarshi ta ba ta, amma tsoronsa take ji. Tana ta tunani, ta ji ana buga ƙofa, cikin murna ta tashi, ta san baƙi tayi sa ɗebe mata kewa. Anty lubabtu ta gani, maƙwabciyar su, da ƙanwarta wadda take karɓar shirin dutse a gidanta, cikin murna tayi musu maraba. Allah ya sa tana da ruwan pure water, ta basu. Ta ce "Anty lubabatu shi ne sai yau zaku zo ko? An barni nikaɗai, ba wanda yake leƙo ni". "Ki yi haƙuri jauhar, tun washegarin kawo ki, nake sintirin neman mai rako ni a gidanku, wallahi fafur 'yan gidanku da 'yan tsukin nan aka rasa masu zuwa su rako mu, wai tsoro suke ji, 'yan gidanku ma wai ba za su rakomu ba, mijinki ɗan daba ne, ni kuwa na ce ko menene zamu zo, sai kwatance suka yi mana". Ta ɗan rausayar da kai ta ce "Shikenan bakomai, yaya saifu ma ya zo, daga ni sai yaran maƙwabta, ni kaɗai nake wuni". Samira ta ce 'Allah sarki, mma dai jauhar ba wata matsala dai ko?" Tayi murmushi ta ce "Babu anty samira, ya shiri kin zo mini da shi?" "Taɓ kina amarya, kawai sai na kawo miki shiri?" Jauhar ta ce "Eh mana, zai din ga ɗebe mini kewa ai, dan Allah idan an samu mai zuwa, ki bayar da yawa a kawo mini, na din ga yi" Anty lubabtu ta ce "Jauhar iyayen neman kuɗi". Samira ta ce "Bar ta ta nema, rayuwar nan ba a zama haka" Miya lubabatu ta soyawa jauhar, mai yawa ta sha naman kaji, da shinkafa da 'yan kayan buƙatu. Jauhar ta ji daɗin hakan sosai da sosai, ta din ga murna, suka wuni tare har la'asar, sannan suka tafi. Suna tafiya ta aiki almajiri, ya sayo mata salak da kayan haɗin sa, ta zauna ta shirya salak ɗin nan, ta juye miyar a tukunya, ta ƙara soyata tayi mata gyare-gyare ta ƙara mata su maggi da kayan ƙamshi ta kammala komai. Ta ɗebarwa yaran da suke shigo mata abincin ta basu, ta ɗebe wani ta rufe, dan abincin da yawa, ta sake turara shinkafar ta zuba a wani flask mai kyau kamar a lokacin ta dafa ta. Tana aikinta, tana jin radiyo a mp. Ta bawa yara kuɗi, suka sayo mata ruwa da lemo mai sanyi. Ta gama aikin, ta share kitchen ɗin, ta kwaso sharar abun da ta ɓata, ta fito kawai ta ga Al'amin a tsakar gida, aikuwa ta razana ta saki abun kwashe sharar tana ihu, ta zubar da sharar a wurin, har zata gudu sai kuma ta tuna kashedin da yayi mata, ta tsaya jikinta yana rawa ta ce "Yi haƙuri, tsorata nayi, ban san ka shigo ba" tayi maganar tana kare jikinta, saboda babu hijjabi a jikinta, bai jira ta gama maganar ba ma, ya shige falo. Ta daɗe a tsakar gida, ta kasa shiga falon ma, ta lallaɓa ta shiga zuciyarta na bugawa da sauri-sauri, gaba ɗaya falon ya gauraye da warin wiwin da yake yi. Ba ya falo, ta shiga ɗaki ta sako hijjabi ta fito, sai dai ta kasa zuwa ɗakin da yake. Wanka yayi ya fito, ya tarar ta ajiye masa sabulun wanka, a cikin wanda ta zo da shi, banɗakin ta kai mas bokiti da ruwa, ga buta ita ma cike da ruwa. Ya gama wankan, ya ɗora soson a kan sabulun yayi fitowarsa, da zai canza kaya kuwa, duddubawa ya din ga yi, da ya gan su a cikin wardrobe, sai da ya watso su gaba ɗaya ƙasa, sannan ya zaɓi wanda zai saka, ya bar su a wurin ba tare da ya gyara ba. 'yar siririyar muryata ya ji a bakin ƙofar ɗakinsa, tana ta sallama. A fusace ya ce "Meye ne?". Ta razana ta ɗan shigo daga bakin ƙofa ta tsuguna, ta ce "Dama tun washegarin kawo ni, wasu sun zo, da kakarka hajiya da wasu, suna nemanka na ce baka nan, suka bani kaya da kuɗi dubu goma, amma na sai maggi da ashana da omo, a ciki baka zama a gida, ban nuna maka ba, shi ne na kawo maka" Ɗan shiru ya yi, jin ta ce hajiya ta zo, ya ji babu daɗi da bai haɗu da hajiyar ba, dan rabon da yaje ya ganta har ya manta. "Ga kuɗin" muryarta ta dawo da shi daga tunanin da yake yi. "Bar nan wurin kafin na yi ball da ke, ba ruwanki da shiga sabgata na gaya miki, tashi ki ware" ta tashi ta ce "Kuɗin fa" banza ya yi mata, ya tsaya yana kallon fuskarsa a mudubin ɗakin. Ganin ba zai kulata ba, ya sanya ta ajiye masa kuɗin, ta tashi za ta tafi, cikin tsawa ya ce "Ke!" A razane ta waiwayo. "Kwashe kuɗin nan ki bar nan" jiki na rawa, ta ɗauka ta ce "To bar mini ka yi" mugun kallon da ya yi mata ya sanya, ta juya da sauri ta bar ɗakin. Ta je kitchen, ta shiryo masa kwanukan abinci a kan tray, amma ta tsaya tana wasi-wasi, kar ta kai masa ya kuma korarta, ta shiga falon tana taradaddi. Ta na shigowa yana fitowa daga ɗakin, take hannunta ya hau rawa, ta ji tana neman ta saki farantin da kwanukan, ta ƙarasa tsakiyar falon, ta ajiye ta ce "Fita zaka yi, ga abinci" ta juya ta koma kitchen ta ɗaukko ruwan roba da lemo, da ta saya masa ta ɗora a kan wani plate ɗin ta kawo. Tana zuwa taga ya zauna ya kame zai ci abincin, kasancewar yana girmama cikinsa, Al'amin yana son abinci, dan haka ba kowane tayi yake wucewa ba. Maimakon ya ɗebi abincin, ya zuba a plate, kawai ya buɗe flask ɗin, ya juye salad ɗin a ciki, ya ɗaga flask ɗin miyar ya girgije a kai, ko kallon cokalin bai yi ba, ya zura hannu ya kama kai loma. Duk da wani irin mugun tsoronsa take ji, amma haka cikin tsoron, ta tsiyaya masa lemo a kofi ɗaya, ɗaya kuma ta zuba masa ruwa. Satar kallonta ya yi, yadda take komai a nutse, sai dai hannunta rawa yake yi, saboda tsoro, mamaki yake yadda take wani zuba masa ruwa kamar ya sakata. Ya din ga tunanin ita kuwa wani zunubi ta aikatawa 'yan gidansu, suka zaɓa su aurar da ita ga shi? Gaba ɗaya yanayinta kalar 'ya'yan hutu ce, irin wanda ba sa son wahalar nan. Sai dai yadda yake auna loma, yana basarwa ba zaka ce, ita yake satar kallo ba. Ta koma can gefen kujera ta zauna ta yi tsuru, gabanta na cigaba da faɗuwa da zarar ta kalleshi, sai dai duk da haka, a ranta ta ji tana son yi masa magana a kan kakarsa, da sauran tambayoyi, duk da miskila ce, amma idan ta samu wuri akwai hira. Sai dai ko kusa ko alama, ba ta ga wannan fuskar ba. Kan ta ankara ta gama zancen zucin, ya kawar da abincin cikin kula 'yar tsakiya, shanye ruwansa da lemo tsaf, ta zuba masa ido, duk da ba abun mamaki bane ba, ta saba ganin maza da shegen cin tsiya, dan tsaf Yaya Saifu zai iya cinye cikin babban flask, dan akwai ranar da suka din ga musu da surayya, ya ce zai iya cinye shinkafa rabin kwano a zama ɗaya, dama taliya leda guda yake cinyewa. Dan haka ba ta yi mamakin yadda ya cinye abincin ba, ya dubi carfet ɗin ta, milk mai haske, ya goge hannunsa a kai ya tashi tsam ya bar mata wurin da kwanukanta a wurin. A hankali ta ce "Na shiga uku, miya a kan carfet ɗina" da sauri ta kwashe kwanukan, ta ɗebo ruwa da omo, ta goge wurin da ya goge mata hannu a carfet, ta koma ɗakinsa, ta sake kwashe kayan da ya zubar. Ya watso su duka gaba ɗaya, ya cire na jikinsa duk ya watsar ya ƙara gaba. Ta sake gyara masa, ta kwaso wanda ya cire, da wanda ta kwashe na wanki ɗazu, ta fito ta jiƙa su zata wanke. Ta koma ta sake sharo falon, sai dai ta ga leda a in da Ya tashi, ta ɗauki ledar, ta taɓa ta buɗe, tana tunanin ko ita ta ajiye wani abun, amma ta ga wani abu kamar ganye a ciki, ta sinsuna ta kasa gane ko menene, kuma a iya tunanin ta, ba ta ajiye ba. Ta samu wani wurin ta ajiye, ta cigaba da aikinta. Sallama aka din ga rangaɗawa a ƙofar gida, ta wanke hannunta ta ce "Waye" Ya amsa da "Ni ne" ta saka mayafi, ta fita ta leƙa. Wani jibgegen ƙato ta gani, jiki duk a murɗe, duk bai kai girman Al'amin ba ba. A ɗan tsorace ta ce "Sannu" Ya ce "Yauwwa, matar gidan tana ciki ne?" Ta ce "Eh meyafaru?" "Ɗan je ki ce mata ana sallama da Boss" Ta yatsuna fuska ta ce "Waye hakan?" "Mai dogon zamani nake nufi, ba shi ne maigidan ba?" Jauhar ta ce "Ba wani mai irin sunan nan a gidan nan, ba sunansa kenan ba" Ya ce "Kee, ni fa nake rako shi har gidan nan, ki ce mini ba sunansa kenan ba?" Ta tsuke fuska ta ce "To shikenan idan ba ka yadda ba"ta mayar da ƙofa ta rufe. Walid ya koma gefe ya kira Al'amin ya ɗaga ya ce "Ya mai laya". Walid ya ce "Na kiyayi mai zamani, maza na zo gidanka wata 'yar cika, ta leƙo ta raina mini hankali, na kusa kwarfeta, na ƙyaleta ne kar na kwafsa" "Wacece ya aka yi?" "Kai na zo nema, ina ta jiranka, yaran nan za su karɓi kaya su rarraba, ba ka zo ba, na biyo ka gida, wata jar yarinya nunar rana mai kama da 'yan china ta ce mini wai ba mai irin sunanka a gidan, na ce mata mai zamani wai ba gidan ba ne" Al'amin ya ce "Ita ce matar gidan fa" "Kai haba maza, wannan ɗin?" "Yarinyar da ta suma, na ce ka saka a kaita Asibiti" Walid ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, maza ka sha kwana wallahi, dama ita ce, kaga rabo, wata 'yar caras beauty ka ji muryarta". "Kai dalla malam, ka buga mata ƙofa, ka ce ta duba in da na tashi, na bar leda ta baka, ka tsaya shirme". Walid ya ce "To meye na yi mini masifa kuma, na ga dai auren dole aka yi maka" katse wayar walid ya yi, yayi ashar ya ce "Ina da wannan, ai kan a ganni a ƙofar gida, sai an sha wuya, kai Aminu kamar ba biladam ba" yayi maganar yana bubbuga ƙofar gidan. Kamar ba zata buɗe ba, ta sake buɗewa cikin mamaki ta ce "Malam lafiya?" "Ya ce ki duba in da ya tashi, ya manta leda ki bani" "Shi wa?" Cikin mamakin yadda take neman raina masa hankali ya ce "Maigidan" "Dan Allah ka yi haƙuri, bai bar mini wannan sallahun ba" Ya ce "Saboda bai bar miki sallahu ba, ba zaki bayar ba?" Ta marairaice ta ce "Idan na baka ya dawo, ya ce mini ba shi ya aikoka ba, kaga bani da abun da zan ce masa". Ya ce "Gaskiya ne, shikenan" ya juya ya tafi, ta mayar da ƙofar ta rufe. Duk da kayan suna da nauyi, haka ta zage ƙarfinta a kan kayan nan, ta wanke su. Sai a lokacin ta kalli window, ta ga mpn da ta ɗaukko masa ta ce "Na shiga uku, da ya ganta fa me zan ce masa?" Ta ɗauka ta mayar masa ɗakinsa Al'amin kuwa duk in da ya juya, sai dai ya yi gyatsa saboda yadda ya ƙoshi. Walid ya je ya samu Al'amin, ya  din ga yi masa mitar yadda jauhar fafur ta hana shi saƙon nan. Yayi ya gama, bai ce masa komai ba, sai sakace da yake yi, yana cigaba da jin ƙamshin miyar da ya ci a hannunsa. "Yanzu mai zamani shikenan yau b za a sayar da kaya ba? Saboda ka yi aure 'yar yarinya ta hana aiki yau?" Al'amin ya kalle shi ya ce "Ƙila" Yayi tsaki ya ce "Yauwwa, na haɗa maka da mp ɗina a kayanka, ka kawo mini kayata kafin ita ma ta ce taka ce ba zata bayar ba" Al'amin ya tuna ya ganta a kan window, kuma ya ga yadda ta gyara masa ɗakin, ya tabattar ɗauka tayi ta kunna. A ransa ya ce 'Ashe ba tsoron ki ke da gaske ba' "Malam magana nake yi maka, a kawo mini mp ɗina. Yunwa ma nake ji, ko zamu je cin garau-garau ne?". Aminu ya miƙe ƙafa ya ce "Sai ka dawo" Walid ya fice yana tunanin asarar da za su yi, na rashin sayar da kayan nan yau, ya san ko zasu dambace da Al'amin, ba zai koma gidan nan ya ɗaukko kayan ba. Ƙarfe tara na dare ya shiga cikin unguwar, tare da su liti, da Walid, sai dai ba su shiga cikin gidan ba, suka zauna a barandar kusa da gidan, suka din ga hira suna shaye-shaye. Jauhar kuwa kamar a cikin falonta suke shaye-shayen, saboda yadda duk gidan ya gauraye da wari. Yau da gari yayi haske ta fito, a falo ta tarar da shi, a kwance a kan doguwar kujera. Ta durƙusa ta ce "Yaya ina kwana" waiwayowa yayi ya kalleta ya kawar da kansa, sai dai ba ta tashi ba. Har ta fitar da ran zai amsa ya ce "Lafiya" Ta miƙo masa leda ta ce "Ga abun da ka manta jiya, wani ya zo ya ce ka aiko shi, ni dai ban bashi ba. Na ga kamar ganyen shayi ne, ko na ɗiba na dafa mana tea?" Afujajan ya kalleta, tashi ya yi zaune ya ce "Da me zaki dafa tea ɗin?" Ta nuna masa ledar tana sunkuyar da kai ta ce "Naga kamar ganyen shayi ne, sai na dafa mana ko jallof ɗin taliya ce?" "Wiwin zaki dafa a matsayin shayi, saboda mahaukaciya ce ke?" Da sauri ta kalleshi ta saki ledar da sauri, sai dai ba ta ji daɗin mahaukaciya da ya kira ta da ita ba. "Dan Allah ka yi haƙuri, ban sani bane". "Jiya mai laya ya zo, ya ce miki yana neman mai dogon zamani, kin ce ke baki san shi ba, to ni ne mai dogon zamani, idan kuma jami'an tsaro ne suka ce miki Viper ni suke nema, idan ki ka cigaba da yi musu rashin kunya kuma, za su sassaraki ne a banza su bawa karnuka namanki" Shagwaɓe fuska ta yi zata yi kuka ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, dan Allah ka bashi haƙuri, ba zan sake ba, dama ban san me zai yi maka bane, shiyasa na ce masa ba kai bane ba shiyasa" Ya saka hannu ya ɗauki ledarsa ya tashi zai fita ta ce "To karin kumallon fa" ko waiwayowa bai yi ba, ya fita. Bayan fitarsa, ta je ta kwaso kayansa da ta wanke, ta ninke su tsaf, ta shiga ɗakinsa, tana shirya masa kayan, ta fito masa da guda ɗaya da zai saka, ta ɗaukko bedsheet tana canzawa katifarsa, kawai ta yi karo da wata irin zabgegiyar wuƙa. Gabanta ya faɗi wuƙar kawai abun tsoro ce. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, jikinta na rawa ta hau kuka, ta kai hannu za ta ɗauka" "Idan ta ji miki rauni, ke ki ka sani". A razane ta ɗago jikinta na tsuma. "Fita ki bar mini ɗaki, bincike ki ke yi mini ko?" Ta girgiza kai ta ce "A'a wallahi, bedsheet zan canza maka na ganta, ba bincike nake yi maka ba" "Fita to" Ta ce "To, ga kaya na fito maka da su, wanda zaka saka". Ya sake tsuke fuska ya ce "Ki fita na ce" Ta zo fita, ta kasa saboda yana tsaye a wurin. Yayi tsaki ya bata hanya, ta fita har da tuntuɓe, a tsakiyar falon ta ga ledar buredi, da sugar da madara da Lipton. Ta lallaɓa ta fita ta kunna gas, ta ɗora shayi. Buga gate ɗin gidan ake yi da ƙarfi, ba shiri ta tafi ta buɗe. Wani matashin magidanci ta gani, a tsaye ya kima uwar hula, ya rufe kunnuwa. Ta gaishe shi cikin ladabi, ya ce "Ina matar gidan?" Mamaki take yi, meyasa mutane suke neman matar gidan idan suka ganta. "Lafiya?" "Eh, megidan muke nema? Sunana malam lawan, ni ne mai wannan gidan na kusa da ke" Jauhar ta yi murmushi ta ce "Allah sarki, baban su halimatu? Ai suna shigo mini". "Eh, mai unguwa yana neman mijinki, ƙararsa muka kai" Ta ce "Subhanallah, laifin me yayi muku?" "Au jira zamu yi sai ya yi kan mu ɗauki mataki, an ce mana mutumin banza ne, kuma da ya zo bai yi mana sallama ba, bamu san da wani irin mutum zamu zauna ba, jiya an hanamu sukunk da warin wiwi, ya tara mana 'yan iska a layi. An gaya mana gawurtaccen ɗan daba ne da ya addabi in da yake, aka yi masa aure mu aka kawo mana bala'i. Gara aje a zauna da mai unguwa da 'yan sanda, ko ya tashi, ko ayi yarjejeniyar zaman lafiya da shi". Jauhar ta ce "Haba malam, bai yi muku komai ba kuma sai a kai shi wurin 'yan sanda, ina laifin mai unguwar ma, in sha Allah ba zai sake sha muku komai a layi ba, kuma ba zai cutar da kowa ba ma. In sha Allah wataran sai labari zai daina". "Ke rufe mini baki kan na kwaɗe ki, nasiha zaki yi mini, ba zamu zauna da mutumin banza da wofi ba wallahi, ya lalata mana yara haka kurum ba" Motsi ta ji a bayanta, tana waiwayawa ta ganshi a tsaye, ashe duk ya ji abun da malam lawan ke faɗa. Da sauri ta leƙa ta ce "Ka tafi kar ka bari ya ganka"ta waiwayo ta rufe gate ɗin tana kallonsa. "Ya tafi kar ya bari na ganshi ko? To ke bari na yi miki abun da zan yi masa". Ayshercool 08081012143 22 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Kafin ta yi wani yinƙuri, ya janyeta daga jikin gate ɗin, sai dai kasancewar ba ƙwari ne da ita ba a kansa, sai da ta kai ƙasa. Ya buɗe ƙofar ya lelleƙa, bai ga kowa ba, tuni malam lawan ya ɓace. Ya dawo ya kalleta, ta sunkuyar da kai, sai murza yatsan ƙafarta take yi, da yake yi mata zafi, saboda faɗuwar da ta yi. Ƙwafa ya yi ya wuceta, ta lallaɓa ta tashi, ta shiga kitchen ta ɗora tea, ta ɗebi miyar nan da su Anty lubabatu suka kai mata, ta ƙara gyarata ta zuba ta kai masa falo. Ya wani maze yana basarwa, nan kuwa jira yake yi, tayi ta kawo masa ya ci. Sai dai yadda yake cin abinci ya goge mata a jikin kujera, ko carfet yana damunta, sai dai idan ya gama ya tashi ta goge. Dan haka ta sayo toilet paper, take haɗo masa da ita, amma ko kallonta ba ya yi, idan Allah ya taimaketa ne, wani lokacin sai ya goge a jikin kayansa kamar wani ƙaramin yaro. Da daddare kuwa kullum, sai ya cika gidan da warin sigari, wasu lokutan ba zai dawo ba, sai sha biyu na dare, ya shige ɗakinsa yayi ta shaye-shaye, da safe kuma idan ta ajiye abinci zai ci, idan ba ta ajiye ba ba zai tambaya ba, kuma ba zai sayo ya kawo ba. Idan za ta gyara masa ɗaki sau goma a rana kuwa, muddin ya shiga sai ya watsar da komai ya ɓata, yayi shaye-shayensa ya bar mata toka da sauran karan sigari duk a ɗakin. Wasu lokutan sai su shafe kwana biyu ba su haɗu ba, gashi zai kwana a gidan, amma ba zai shigo ba sai ta yi bacci, duk da wataran ba ta baccin sai ta ji shigowarsa, asubar fari kuma sai ya fice, ranar da ya ga dama kuma, sai ya bari gari yayi haske, ko za ta bashi abinci, dan sai yanzu ya fuskanci abincin waje wasu lokutan ga ƙaurin hayaƙi gashi ba sa jin sinadaran ɗanɗano, nata kuwa har cikin kansa yake jin su. Yau ma dawowa ya yi rana tsage-tsage, walid ya sayo musu abinci, yana fara ci ya ji babu daɗi, ya ajiye ya ce gida zai tafi. Walid ya ce "Da ranar nan tsaka zaka fi gida?" "Eh" ya amsa a taƙaice. "Lallai, na fuskanci lamari yana ta daidaita to Allah ya sa mu ji alkhairi ya kawo zuriya ɗayyiba" Ya haɗe rai ya ce "Mai laya" Walid ya ce "Sorry maza, na kiyayi mai zamani" ya fice ya tafi gida. Jauhar tana ta lissafin kuɗin hannunta, sun kusa ƙarewa, girkin ma duk da dabaru take yin sa, ga gogan babu ruwansa sai dai ta dafa ya lashe. Da 'yan dabaru take yin ɗan wake yau, ta aiki almajiri ya sayo mata kabeji da cucumber, tana jiran dawowarsa, Al'amin ya dawo, a duk lokacin da za ta ganshi sai ta razana, gashi ba sallama yake yi ba, ya hangota da tukunya a kan gas, ya yi ajiyar zuciya ya san zai ci abinci. Ya shiga ɗakinsa, ya tarar ta sake wanke masa kaya, ta gyara ɗakin tsaf. Tsaki yayi ya ce "Ita dai wannan an yi 'yar wahala" Ya daidaici lokacin da ta gama girki, ya dawo falo ya zauna, aikuwa sai ga ta abinci bakinta ɗauke da sallama. Bai amsa na sai Alla-alla ta kawo ta ajiye, saboda yadda ƙamshin manjan, ya cika masa hanci. Ta ajiye masa ya haɗa abun sa ya fara ci. Ta zauna a gefensa, cikin fargaba ta ce "Yaya" shiru ya yi mata, yana haɗiye ɗan wakensa da hurhuɗu biyar-biyar. Ta sake cewa "Yaya magana nake dan Allah abu zan tambayeka". "Malama sunana Aminu, kar ki sake ce mini wani Yaya" a ranta ta ce 'Ai na san a rina' A zahiri kuma ta ce "Ai ba zan iya faɗar sunanka ba, ya za ayi na faɗi sunan mijina kamar mara ɗa'a" sai ya ji abun wani banbarakwai wai mijinta. "To me zan din ga ce maka?" Ba ta jira amsar sa ba, dan ta san ba zai amsa ba, ita kuma zaman kuramen nan da suke yi ba son sa take yi ba, ace kana zaune a ƙarƙashin mutum, amma ba zai kulaka ba. "Na ji abokanka suna ce maka boss, ni kuma sai na ce maka master, idan na ce master zaka amsa, ko nima boss zan ce? Tun da ba ka son yaya?" Ta tambaye shi tana murmushi ba tare da ta kalli in da yake ba, saboda kwarjinin da yake yi mata, yanzu haka ma ƙarfin hali kawai take da take yi masa magana. Kallonta yayi, tana murmushi dimple ɗin ta na side ɗaya ya lotsa, ya gane dakiya kawai take yi, amma a tsorace take yi masa magana. Duk da bai bata amsa ba, amma matsern da ta ce zata din ga kiransa da shi, ya so yayi murmushi, amma yaƙi ya sha kunu, yana suɗe kwanon ɗan wakensa. Cikin hikima ta ce "Da da sauran garin ɗan waken nan, da na dafa maka wani, ko na ƙaro maka?" "A'a" ya ajiye kwanon, cikin sauri ta miƙa masa wani tsumma mai kyau, ta ce "Gashi ka goge hannunka, manjan yana da kamu, sai mu je waje na zuba maka omo ka wanke sosai" ya karɓa ya goge, ya koma ya kashingiɗa yana duba wayarsa mai madannai. "Na ce, dan Allah sonake na shiga maƙwabta na yi musu sallama na tare, wai haka ake yi, ka ga mu bamu cewa kowa mun tare ba" "Sauka lafiya" ya faɗa ba tare da ya kalleta ba. "Yauwwa na gode sosai master, bari ayi la'asar, sai na je. Yauwwa mutumin ɗazu ya ce wai mai unguwa na nemank..... Ba ta ƙarasa ba ya tashi, dan surutunta ya fara isar sa. Bayansa ta bi da kallo, 'Da sannu wataran zaka tanka mini ne, ni ba zan iya rayuwar zaman kurame ba' tayi maganar a hankali. Huɗu da rabi, bayan ta yi la'asar, ta leƙa ɗakinsa ta ce masa za ta fita, ta tarar yana salla. Wata irin ajiyar zuciya ta yi, tare da hamdala a zuciyarta, ba ta taɓa tsammanin yana kai goshinsa ƙasa ba. Ta zauna a bakin ƙofar tana kallonsa, duk da shaf shaf yake yi, kuma azahar da la'asar ya haɗa a lokacin, amma ta ji dadin ganin yana salla. "Master bari na je, idan ka idar ka sani a addu'a, Allah ya sa ka daina jin haushina, ban san me nayi maka ba" dama ta san ba amsawa zai yi ba ta fita. Matasan 'yan mata ne su biyu a gaban rahila suna cin abinci, da alama daga makaranta suka dawo, domin kuwa bayansu jibga jibgan akwatuna ne, na 'yan makaranta. "Umma, nifa haryanzu na kasa daina mamaki, wai yaya ne yayi aure? Wai dan Allah ya aka yi aka samu aka bashi 'ya a yadda yake? Kuma ba a bari mun dawo ba aka yi bikin?" Rahila ta ce "Ke dallacan, waye ya ce miki abun na shiri ne shahida? Neman mafita nake ba shiri faka-faka na saka aka samo wata yarinya ya je can ya ƙarata, ya ƙara sako mini yaro a gaba, irin kallon da yake yi mini, tsaf zai halakka ni, cikin ikon Allah tun da aka yi auren, ban sake ganinsa a gidan nan ba, ya samu mace yayi luf" Shahida ta ce 'Ni wallahi mai tsautsayin da aka aurawa nake jin tausyai, yaya za ta yi da shi dan Allah dan Annabi?" Amira ta ce "Ke ina ruwanki ne shahida, ina ruwanki da ko ma wa ce ta aure shi, ba dai an samu ya tafi na, case close". Shahida ta yi murmushi ta ce "Ina ne gidan nasa ne?" "Yana can gidansa na ɗorayi, ba kuma cewa na yi ki je ba, kar abun da ya kai ki gidansa, balle ya lallaɓa ya dawo mana nan ya je can su ƙarke". "Ahh haba umma, sai mu yanke alaƙa da shi duka kenan? Yayi aure muna school kuma mun dawo ba zamu ganshi ba?" Amira ta ce "Wallahi a garin shishshigin nan da ki ke masa, zai kassara rayuwar ki, ki yi ta shige masa yana yarfaki" "Wallahi ki ka je gidansa ma sai na ci ubanki shahida, na gaya miki, ke baki san sai ku kasa auruwa ba saboda mugun halinsa da mummunan tabon da yake da shi ba a unguwar nan?" Shahida ta ajiye cokalin hannunta ta ce "Umma, shi fa jini ya fi ruwa kauri, the only male brother i have, sai ki ce sai na yanke alaƙa da shi?" "Au jayayya zaki yi da ni? Shi Abban uban meye idan ba yayanki ba?" Ta tashi ta ce "Ai ba babanmu ɗaya ba, Yaya Al'amin kuma babanmu ɗaya, kowane ina son sa" Rahila ta ce "La ila ha illalahu Shahida " Amira ta ce "Dan Allah umma bar shashasha, za ta gane kurenta ne" Rahila ta cigaba da salallami, a kan yadda ke adawa da ita wasu lokutan a kan Al'amin. *** Juahar gidan malam lawan ta fara shiga, wato gidansu halimatu da walida, yaran da suke zuwa tayata hira, suka gaggaisa da maman, sannan su halimatun, suka rakata sauran gidajen maƙwabta, tayi musu sallama. Har wurin masu kayan miya, da masu shaguna suka nunnuna mata da wurin makarɗe. A bayan gidan suka je har gidan wata tela, da har da yaranta, su na shigarwa jauhar, suka gaisa jauhar ta tarar da yaran suna stone work a jikin ɗinki, har ta karɓa tana taya su, saboda a rayuwarta tana son sana'oin hannu suna matuƙar burgeta. Take cewa matar, idan an samu stone work ta din ga aika mata da shi tana yi mata. Matar ta ce 'To nawa zan din ga baki, dan kuwa ina samun aikin su sosai da sosai" Cikin tsananin murna, da jin cewa ta samu abun yi, ta cewa matar, ko nawa ne ta bata, tana son za ta din ga yi, nan hira ta ɓarke, take gaya wa matar, ta iya shirin dutse, har adon da ake yi da shi a jikin ɗinki, duk zata iya, suka yi yarjejeniyar matar zata din ga bata ta yi mata. Ganin hadari ya fara haɗowa, ya sanya ta yi mata sallama, ta koma gida, sai dai tana komawa, ya zura takalmansa zai fice, ta ce masa kar ya fita, hadari ne a garin, amma ba ta gama rufe baki ba, ta ji ya buɗe ƙofa ya fice. Ta kawar da abun da zata kawar, ta rurrufe ko ina, ta laluba ta ɗauki mp a in da ta ajiye, ta tarar ya ɗauke kayarsa, ta ce "Da sauƙi, tun da ba ka yi mini faɗa ba". Ruwan sama aka yi, kamar da bakin ƙwarya, ga wata irin iska da ta jefa jauhar, cikin razani da tashin hankali, yadda kwanon yake ƙara ji take tamkar zai kwashe ne, saboda ƙarfin iskar da ruwan. Ta takure wuri guda, tana ta addu'a, kasancewar lokacin da ake ruwan sama, lokaci ne na karɓar addu'a, mafi yawan addu'arta a kan Al'amin ne, da take masa fatan shiriya. Ko da ruwan ya tsagaita, ta fito falonta, ruwa ya shigo sosai, ya jiƙe ɗakin, ta buɗe ƙofar falon, rashin kyakykyawan magudanan ruwa, ya sanya kwatocin layin yin ambaliya, duk suka shigo mata gida, gashi ba ga da rariyar kirki, sai ta banɗkuna, dan haka babu wurin da ruwan zai fita, tsakar gidan ya shafe da ruwan kwatami, falonta ma duk ruwan ya shigo, gashi idan aka yi ruwan, tsigar jikinta tayi ta tashi. Haka ta samo kwano, ta din ga ɗibar ruwan tana zubarwa, ta naɗe carfet ɗin ta, ta jingine, sai zallar buhun da aka shimfiɗa a ƙasa, ta din ga kwarfe ruwa a falon nan. Ta je ta yi sallar magariba, Allah ya sa ruwa bai shigar mata bedrooms ba. Ana sallar isha'i sai gashi ya dawo, ya tarar da ita, fitilarta babu batirin kirki, duk tayi duhu, sai kwashe ruwa take a falo. A ransa ya ce "Iyayenki ne suka ja miki" tayi masa sannu da zuwa, ta cigaba da aikinta, har zai wuce ya dawo ya karɓi kwanon, ya haɗe mata kujerunta wuri guda, ya kunna fitilar ƙaramar wayarsa, ya ƙarasa kwashe ruwan. Shi kansa ya san gidan nan kango ne, yana buƙatar gyara sosai, bai ci ace har an saka mutum a ciki ba, amma da iyayensa da na ta, ya rasa wannene uban garajen da ya saka aka yi haka. Ya ɗaɗɗaga labulayen, saboda ɗakin ya sha iska, daga nan ya tafi makwancinsa, ta tafi nata. Da safe ruwan duk ya tsane, amma sai ƙanƙame jikinta take yi, ƙarnin ruwa da ya kwanta ya din ga damunta. Haka nan ta daure, ta gyara gidan, ta zuba miya ta yi jallof ɗin macaroni, kasancewar falon a jiƙe yake, da danshi, da sauran Lipton ɗin jiya, ta dafa shayi har da su citta ta yi sallama a ƙofar ɗakinsa, bai amsa ba dama labulen a ɗage yake ta shiga. Ta ajiye masa ta ce "Ina kwana?" Ba ta jira ya amsa ba, ta haɗa masa tea, ta tashi ta fita. Aka jima ta dawo, ta shiga banɗakinsa ta wanke, ta ɗauki bokiti ta dawo, ta haɗo ruwan zafi na wanka, ta kai masa banɗakin ta ce "Master ga ruwan wanka nan na kai maka, mai ɗumi ne" idan ta ce mastern nan, sai ya ɗaga kai ya kalleta. Ta ce "Yauwwa, master zan kafa ƙusa a toilet ɗin ka, idan ka gama wanka, ka dinga saƙale soson, idan ba haka ba sabulun narkewa yake yi, sai ka ga ya ƙare da wuri" Ta zagaye shi, ta fara tattare kayan duk da ya watsar a ɗakin kamar ƙaramin yaro. Ya gama cin abincin sa, ya fara shan tean, yana jin yadda ƙamshin da yajin citta yake ratsa shi yana yi masa daɗi. Yana zaune ta gyare ɗakin, ta kukkuna masa turaren wuta, sai dai kafin ta ƙarasa, ya kunna sigari a ɗakin. Sai da ranta ya sosu, akwai sauran warin ta jiya da daddare ma da ya sha, ta gama aikin ɗakin, ta kunna turaren wuta, ya kuma kunna wata sigarin. Ta maze ta ce masa "Ruwan wankanka, kar ya huce fa, na ga garin da sanyi haryanzu, idan ka yi wanka da na sanyi, zaka yi mura" A hasale ya ce "Ke, fita ki bar mini ɗaki, kin gama tsegumin ai, kin sakani a gaba kin ga abun da nake yi, to fita ki bar min ɗaki, ba zan wankan ba" Ba ta sake cewa komai ba, ta juya ta fice, ta cigaba da ayyukan ta, tana tsaka da wanke-wanke, ya fito da sauri, hannunsa riƙe da waya yana cewa "Kar ku raga musu, gani nan zuwa" ta miƙe tana kallonsa, amma ta kasa yi masa magana. A haka yana ƙaurin sigarinsa da komai, ga kayan da su ya wuni jiya, ya wayi gari da su, amma bai canza wasu ba, ya fice cikin matsanancin sauri. Ta koma ta cigaba da aikinta, tana addu'a Allah ya sa ba wani rashin jin zai je yayi ba. Baba yana gida, aka aiko ana sallama da shi. Yana fita ya tarar da 'yan uwan Alhaji mu'azzam da suka kawo kuɗi. Suka gaggaisa, ƙanin mahaifin Alhaji mu'azzam ya ce "Gamu mun dawo, ɗanka ne ya dawo da mu, ya ce a bayar da haƙuri, kar a ji mu shiru, ayyka sun yi masa yawa, ba zai samu dawowa nan kusa ba, shi ne ya ce mu zo ayi magana, a ƙarasa shirye-shirye kawai, ayi auren a tura masa ita can". Gaban Baba ya faɗi jikinsa a sanyaye ya ce "Alhaji dama ko da baku zo ba, zan neme ku ni na zo, an sami matsala ne, zan dawo muku da kuɗin aurenku". Suka yi turus gaba ɗaya suka ce "Wace irin matsala ce haka?" "Yarinyar nan, yau ta kusa sati biyu, ina mai baku haƙuri, a bashi haƙuri dan Allah. Zan kawo muku kuɗin aurenku" "Amma wani abun yayi ne, ko wani laifin shi mu'azzam ɗin yayi?". Baba ya ce "Ko ɗaya, ka san matar mutum kabarinsa, mu'azzam bai yi mini komai ba, dan Allah a bashi haƙuri" Suka ce "To shikenan, Allah ya tabattar mana da alkhairi". Suka amsa da "Amin" Baba ya ce "Ku bani account number, na mayar muku da kuɗin auren" Ɗaya daga cikin su ya ce "A'a, a bar wannan maganar sai ya dawo tukuna, Allah ya basu zaman lafiya" Ya amsa da "Amin". Bayan la'asar yara duk suna islamiyya, babu 'yan aike, ta ce bari ta fita ta sayo maganin sauro, idan ya dawo sai ta gaya masa. A ƙofar gida suka haɗu da maman su halimatu a waje da wata maƙwabciyar su, suka gaisa ta ce "Maman halimatu, ba ku shigo mini mun gaisa ba haryanzu". "Wallahi Amarya, ba ƙi muka yi ba, kin sa yanayin mijin naki sai a hankali, abun da tsoro, kar wani abu ya faru". Ranta bai yi mata daɗi ba ta ce "Haba dai, ina ruwansa da ku? Kawai dai a shigo a gaisa, shikenan a gaida su halimatu" tayi gaba zuciyarta babu daɗi, a duk lokacin da ta ji an aibata shi, sai ranta ya sosu. Har dare ba ta sake ganin Al'amin ba, gashi ita ba waya ba, wasa-wasa har dare yayi babu Al'amin babu dalilinsa har garin Allah ya waye, bai kwana a gida ba. Sai abin ya fara damunta, gashi ba ta san a ina za ta ganshi ba. Abu kamar wasa, aka sake shafe wuni, aka shiga kwana na biyu, babu shi babu labarinsa, nan fa hankalinta yayi mummunan tashi, gashi ba ta san wa za ta nufa ta gayawa ba. Maman halimatu ce tayi sallama, Jauhar ta saka hijjabi ta fito tana murmushin yaƙe ta ce "Maman halimatu, sannu da zuwa shigo" "A'a ba shigowa zan yi ba, abbansu yana nan bai fita ba, bai san ma na shigo ba na ce kin kuwa san an kama mijinki?" Gaban Jauhar ya faɗi ta ce "Yaushe? A ina? Waye ya gaya miki?" "A bakin Abban su halimatu na ji, cune suka yi masa aka kama shi, amma dan Allah kar ki gaya masa wanda suka saka aka kama shi ɗin dan Allah, na gaya miki ne na san baki sani ba". Tuni idon Jauhar ya cika da hawaye ta ce "Eyya, meysa abban su halimatu yayi haka? Wallahi babu abun da zai yi wa wani, ba ruwan shi da kowa idan ba taɓa shi aka yi ba, ina aka kai shi? Dan Allah ki gaya mini, ina gidan ban san ina zan nufa ba ma". Tayi ƙasa da murya ta ce "Yana anti daba can aka kai shi". "Menene anti daba kuma? Ina ne?". "Can in da ake kai 'yan daba, ki shirya ki je ki duba shi". Ta ce "To na gode" bayan tafiyar maman halimatu, take ta ji haushin malam lawan ya kamata. Tayi tunanin ko gidansu za ta je, ta faɗa, amma sai ta ga idan tayi hakan, kamar ta tozarta kanta ne, dan haka ta fasa ta ɗora girki, ta gama ta shirya, ta zuba a flask, ta bi kwatancen da maman halimatu tayi mata. Su kansu yanayin jami'an tsaron wurin, tsoro suka bata, ba ta taɓa zuwa police station ba, ta gaishe su cikin girmamawa sannan ta ce "Dan Allah wani nake nema" "Wa kenan?" Wani ya tambayeta. "Al'amin sunansa" Ɗan sandan ya ce "Anya, babu wani mai irin wannan sunan da muka kama". Ta ce "Dan Allah nan aka ce mini an kawo shi, dan Allah officer ka duba mini" Na kusa da shi ya ce "Ko viper take nufi?" Ta ce "Eh shi, mai dogon zamani" "Ya aka yi me zaki yi masa?" "Wurinsa na zo, maƙwabciyata ta ce mini cune aka yi masa aka kama shi, wallahi bai yi komai ba". "Ke ya aka yi ki ka san bai yi komai ɗin ba? Wacece ɗin sa ke, ni tun da muke kama shi ma, ban taɓa ganin wani ya zo wurinsa ba, idan ba ire-iren sa ba ko yaran ubangidansa ba" Ta ce "Mijina ne" Saroro suka yi suna kallon jauhar, kyakywar yarinya ƙarama da ita. "Ke kuma auren soyayya ku ka yi? Jama'a kun ga matar Viper, yaushe ne kuwa zuwansa na ƙarshe aka fito da shi aka ce aure yayi" waiwayowa suka yi suna kallonta, ta sunkuyar da kai tana fatan Allah ya sa su bar ta ta ganshi. Ɗaya daga cikin su ya ce "Ku fito da shi, ta ganshi, amma dai Viper yayi asara, daga aurensa ya saka 'yar mutane fara sintiri saboda shi". Saroro yayi da ya hangota cikin hijjabi, 'yan sandan suna yi mata tambayoyi. Tana ganinsa tayi ajiyar zuciya, ya ƙaraso gaban kantar ya kalleta ya ce "Me ya fito da ke?" "Kwana biyu baka nan, ban san in da ka ke ba, sai yau ban san kama ka aka yi ba" Ya sake kallonta ya ce "To ware ki koma" Jauhar ta ce "To in koma, kai fa ba sakinka za su yi mu koma ba?" Al'amin ya ce "Ki tafi na ce, kuma kar ki sake zuwa wurin nan kina mace, ware" haushi ne ya kamata, yadda yake korarta, shi ba ayi masa abun arziki sai hantara. Ta ɗora leda ɗuake da flask ɗin Abinci ta ce "Gashi abinci ne na kawo maka" sai da ya ɗan yi shiru yana kallonta. Tun da ya fara rashin jin sa, babu mai tunawa da shi, ya kawo masa ziyara ko abinci, idan ba su walid ba, sai kuma ita yanzu. "Ahh yau zamu ci girkin amarya, amma hajiya sai kin fara ci kafin ya ci" Bai saurari ɗan sandan ba, ya ɗauki abincinsa ya koma gefe. Ya buɗe, ta yi sauri ta zagaya, ta huda ruwa pure water, ta ce masa "Ka fara wanke hannunka" Kamar ya shareta, sai kuma ta zuba masa ya wanke, ya saka hannu ya fara cin abincin. "Akwai sauro ne wurin? Na ga kamar ya cijeka, jikinka duk cizon sauro?" "Mmm" ya amsa yana cigaba da cin abincin. "To yaushe zasu sake ka, kar ka yi rashin lafiya, saboda cizon sauro" shi dai yayi shiru yana cin abun sa. Ya gama ci ta bashi ruwa, ya karɓa ya zuƙe, ta ƙara masa wani ya shanye. Ta ce "Officer, to zaku sake shi? Bai yi komai ba" "Ke, da wiwi muka kama shi da ƙwayoyi, sai kuma ki ce bai yi komai ba? NDLEA zamu kai shi". Jauhar ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, dan Allah ku yi haƙuri, ba zai ƙara ba in sha Allah, Master ka basu haƙuri su ƙyaleka mu tafi" miƙewa yayi tsaye, ya nufi hanyar komawa cikin ceil. "Officer to, idan na sayo maganin sauro da ashana, zaku bar shi ya kunna?" Gaba ɗaya sai ta basu tausayi, ya ce "Sayo" Ta juya ta fita da sauri, shi kuma ya tsaya ya waiwayo ya bi bayanta da kallo. "Viper, wai dan Allah ka bamu labari, wurin wani bokan ka kai 'yar mutane da iyayenta, suka aura maka 'yar su?" Shi dai ya ƙarasa ya koma cikin ceil, yayi zamansa, ba a jima ba, sai gata da maganin sauro, da ashana. Suka karɓa a nan kan kanta, suka ce ta tafi. "Dan Allah ku bari na sake ganinsa" "Ke wuce ki bar nan, da ki ka samu ma aka bari ki ganshi?" Ba ta karaya ba ta sske cewa "To ana bashi abinci? Ko ina kawo masa na dare ma" "Au uban wa ki ka ajiye da zai bashi abinci a nan? Ware ki tafi" Jiki a sanyaye ta ce "To, zan tafi ga wannan dan Allah officer ko buredi ku bashi" ta ajiye musu ɗari biyar sannan ta ce "Dan Allah kuma ku yi haƙuri, kar ku kai shi NDLEA, dan girman Allah in sha Allah zai daina, ba zai ƙara ba ma dan Allah" "Ki je ki kawo dubu hamsin, sai mu sakar miki shi" Tayi shiru, har ga Allah ba ta da ita, ba ta da dalilinta amma ta ce "To zan kawo, amma dan Allah kar ku kai shi, zan kawo muku in sha Allah" Ta fito daga wurin, tana tunanin ina zata nufa ta samo dubu hamsin a sake shi. Ayshercool 08081012143 23 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Tun da ta hau adaidaita sahu, tunani take yi, yaya za ta yi ta samu dubu hamsin ta kai, a sako shi. Ta san muddin aka kai shi NDLEA case ɗin tsayi zai yi, ba zata musa an ganshi da kayan maye ba, tun da yana sha. Ta koma gida tayi salla, amma abun duniya ya isheta, ta kasa ko cin abinci, tausayinsa duk ya cika mata zuciya, jikinsa yayi ruɗu-ruɗu da cizon sauro, gashi almu sun nuna ba abinci ake ba shi ba. Baba kuwa abun duniya ya dame shi, yadda ya ji kunya a idon iyayen Alhaji mu'azzam, ace sun kawo kuɗi sun gama magana, amma ya aurar da ita ga wani, ko gaya musu bai yi ba, ya rasa me yake yi masa daɗi, har sai da zakiyya ta fahimta ta ce "Baban su Saifu, wai lafiya kuwa? Tun da ka yi baƙi jiya, gaba ɗaya ka rasa nutsuwar ka" Ya sauke numfashi ya ce "'yan uwan Alhaji mu'azzam ne, suka zo suna bayar da haƙuri a kan jin su shiru da aka yi. Wai za ayi mata visa ayi auren a tura ta can" Waro ido tayi ta ce "Sai kuma ka ce musu me?". "Na aurar da ita" yayi maganar a sanyaye yana sake jinjina wautar da ya yi. "Ba a haka fa, sai ka ce musu Allah ne ya ƙaddara a hakan, amma akwai yayyenta, ko hafsa ba sai a maye gurbinta da ita ba, hafsa ba ta fi jauhar komai ba ma? Ai bai kamata a bari ya tafi haka ya tsallake gidan nan ba". "Zakiyya, kun saka na yi abun da yake damuna, na cuci 'ya ta ba gaira babu dalili, na aurar da ita ga mutumin da ba na kirki ba, na rasa yadda aka yi, lamarin nan ya faru, kunyar haɗuwa da jauhar ma nake yi, na kasa komawa gidanta, zuciyata zafi take yi mini" Zakiyya ta ce "Jauhar fa an gama babinta, sai a fuskanci 'yan uwanta, bai kamata a bari mutumin nan ya tafi haka ba" "Zakiyya, dan Allah ki bari na samu nutsuwa, ni ban san ma meyake damuna ba, dan Allah ki bari na ji da abun da yake damuna" Ta kwantar da murya ta ce "Babu wani abu fa da yake damunka, kai ne ka ke neman ɗorawa kanka matsala, amma komai mai sauƙi ne, idan ya dawo ba sai a lallaɓa shi a bashi Hafsa ba ya aura". Baba ya ce "Na ji, amma dai yanzu ki ƙyaleni" ya ɗauki hularsa ya saka ya fita. A tsakar gida ya tarar da su surayya, aiki duk ya kacame musu, aiki ba aiki, wanda da jauhar na nan, ita kaɗai take yi suna mimmiƙe kamar kifi a fridge. Suna ta yi masa a dawo lafiya, ya dawo da baya ya tsaya, ya kalle su ya ce "Surayya, kun je gidan ƙanwarku kuwa kun ganota?" Duk suka yi shiru, suka kasa amsa masa. "Yakamata ku je ku ga in da aka kaita, ita ma ta ji daɗ". Mama ta fito daga kitchen ta ce "A'a fa, ka san dai yadda mijinta yake, ba zuwa gidanta ne ba za ayi ba, kar mutum ya je ya illata shi". Yayi shiru bai ce komai ba. Jauhar kuwa kasa nutsuwa tayi, har sallar nafila tayi mussaman tana fatan Allah ya sa kar a kai Al'amin NDLEA. Duk yadda ta kai ga tunani, ta rasa mafita, bacci ya gagareta, a gidanma ya ta ƙare da sauro, ina ga shi da yake can, ta yi ta fatan Allah ya sa su saya masa buredin nan su bashi, sai kuma ta tuna ba ta bayar da kuɗin da za a saya masa ruwa ba, gaba ɗaya ta shiga damuwa, haka har garin Allah ya waye. Ta ji ƙarar babur ɗin malam lawan alamar ya fita, tana ta tunanin ko shiga za ta yi gidan, ta yi wa maman halimatu magana, ko akwai taimakon da za ta iya yi mata. Tana cikin tunanin, maman halimatu ta shigo, suka gaisa jauhar ta ce "Yanzu nake tunanin zuwa gidan wurinki". Maman halimatu ta ce "Yaya kin same shi ɗin?" "Eh yana can, sun ce na kai dubu hamsin a bayar da belinsa, amma wallahi bani da ita" "To yanzu ya za ayi?" Jauhar ta ce "Wallahi ban sani ba, shi nake ta tunani" "To ki kira gidanku mana ki faɗa" ta girgiza kai ta ce "A'a, daga yin auren sai na fara kai musu complain, a'a gara na rufa masa asiri na samu ya fito" "Aikuwa Jauhar sai ki yi tunanin in da zaki samo kuɗi". Tayi saurin cewa "Dan Allah ko akwai wanda zaki haɗa ni da shi, ya sai carfet ɗina?" Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Eh akwai wata dillaliya, kusa da titi gidanta yake" Cikin ɗoki jauhar ta ce "Mu je ki rakani maman halima". "Shikenan, amma Jauhar kina me ki ka auri mutumin nan, gashi daga aurenku kin fara wahala, da kyanki da ƙuruciyarki, kin auri wanda zai wahalar da ke". Jauhar ta yi murmushi ta ce "Maman halimatu ku daina aibata shi dan Allah, ku din ga yi mana addu'a" "To Allah ya kyauta" Jauhar ta saka hijjabi, suka tafi gidan dillaliya, sai dai bata nan, aka kirata a waya, ta ce sai yamma zata dawo, zata biya gidan maman halimatu, su je gidan Jauhar ɗin. Wunin ranar jauhar kamar ta yi hauka, saboda dillaliya ba ta zo ba, sai tunanin halin da yake ciki take yi. Sai wajen ƙarfe biyar sannan ta zo, ta ga carfet ta ce zata saya dubu goma. Maman halimatu ta ce "Haba sahura, wane irin dubu goma, bai fi sati biyu ba ca carfet ɗin sabonsa dubu kusan sittin ne fa". "To ku ɗauka ku mayar kasuwar mana, tun da an shimfiɗa ai ya zama taoho". Jauhar ta ce "Bakomai na yadda" ba ta da burin da ya wuce ta ga Al'amin ya fito. Sahura ta ce 'Saboda kin ban tausayi, na saya dubu sha biyu, bari na baki kuɗin. Maman halimatu ta ce "Wallahi sahura shiyasa da yawanku ba kwa arziki dillali, duk cuwa-cuwar ta ku, a tsiyace ku ke mutuwa" Sahura ta ce "Oho miki dai" Ganin ta fito da kuɗi da yawa, ya sanya jauhar shiga kitchen ɗin ta, ta ɗauko blender da set na tukwanenta masu kyau, ta cewa dillaliya su ma ta saya. Maman halimatu ta ce "Jauhar, idan 'yan gidanku suka gane kin sayar da kayanki fa?" Sahura ta ce "Wallahi uwar su halimatu ke 'yar baƙin ciki ce, ke kika saya mata?". Jauhar kamar ta yi kuka ta ce "To ya zan yi maman halimatu, bana son zamansa a wurin nan, sauro ma kawai ya ishe shi" Sahura ta ce "Allah sarki yarinya, Allah ya mayar da alkhairi, idan an tashi sayar da wasu ma ki kira ni" Da ƙyar ta bawa Jauhar dubu ashirin da huɗu gaba ɗaya. Wanda a ƙalla sun kai kayan dubu ɗari da wani abu. Ƙoƙarin nemo wani abun take, maman halimatu ta hanata, ta ce ta bari gobe ta je station ɗin, ta basu haƙuri ta ce musu abun da take da shi kenan. Jauhar ta ce "Ki na ganin za su karɓa kuwa?" "Za su karɓa mana, ai kin yi ƙoƙari" kamar ta janyo wayewar gari, ta din ga addu'a Allah ya sa su karɓa su sake shi. Da wuri ta gama komai, wurin ƙarfe goma da rabi ta fita, shi ma maman halimatu ce ta hanata fita da wuri, ta ce mata ba da wuri suke zuwa ba. Suna ganin Jauhar suka ce "Madam ya aka yi ne? Kin sake dawowa ganinsa ne?" Ta ciro kuɗin ta ce "Gashi dan Allah yallaɓai ku sake shi, sukaɗai na samo dan Allah ku yi haƙuri" Ya zuba mata ido ya ce "Shekarar ki nawa ne?" Ta ce "Na kusa shiga sha bakwai, dan Allah ku yi haƙuri" "To ai ba zamu iya baki belinsa ba, kin ga mace ce ke, kuma yarinya, Allah ya sa ya daina abun da yake ko dan saboda ke, karɓi kuɗinki, ba zamu sake shi a kan wannan ɗan kuɗin ba, kotu ma zamu kai shi" Kawai ta saka kuka, "Dan Allah ku yi haƙuri, ba zai ƙara ba dan Allah kar ku saka a kai shi prison" Ɗaya daga 'yan sandan ya ce mata "Yi haƙuri ki daina kuka, da wasa yake yi miki, an zo belinsa ma, ke ki ke tayar da hankalinki, ko mun kama shi zamu sake shi" Kasa daina kukan tayi, hannunta riƙe da kuɗin, wani ɗan sanda ne ya fito, da alama babba ne, bayansa kuma walid ne da Al'amin da wani mutum. Wata irin ajiyar zuciya ta yi, ta zubawa fuskarsa ido, da take a ɗaure babu walwala. Walid ya ce "Kai Viper, wannan ce yarinyar da na tarar a gidanka, tayi mini rashin mutunci" "Wannan fa me aka yi mata take kuka?" "Sir, matar Viper ce" ya kalleta ya ce "Hajiya me aka yi miki ki ke kuka?". "Ce mini suka yi na kawo dubu hamsin za a sake shi, na kawo kuma suka ce mini wai kotu za su kai shi" ta ƙarasa maganar tana sake fashewa da kuka cike da yarinta. Ya kalli 'yan sandan ya ce "Waye ya ce ta kawo dubu hamsin" "Sorry sir, dan ta daina zuwa aka gaya mata haka" Nan ya hau yi musu faɗa, suka din ga bayar da haƙuri, Al'amin kamar bai santa ba, yayi gaba. Da sauri ta bi bayansa, tana ta yi masa magana yayi shiru. Walid ya ce "Haba mai dogon zamani, ka tsaya ka saurareta mana" A fusace ya waiwayo ya hau ta da masifa "Ban ce miki kar ki sake zuwa wurin nan ba? Kin san suwaye ake kawowa wurin nan? Mutuncinki ne a ganki a nan?" Sai da ta ja da baya a tsorace ta rufe fuskarta, saboda razana da masifar da yake yi mata. "Wai Aminu meyasa ka ke yin haka? Da uban waye ya damu da kai, yake ta taka? Macen kenan haka zuciyarsu take, ko dan matar gidanku ba ta da kirki kowa ma haka yake?" Tsaki ya yi yayi gaba. Walid ya ce "Yi haƙuri mu je, rabu da shi ya ƙarata, kar ki sake tayar da hankalinki saboda shi" suka tari a daidaita sahu suka tafi gida. Da suka je gida, ta shiga gidan ta bar shi da Walid. "Aminu, dan girman Allah ka rage jaraba, kalli yadda duk ta rikice saboda kai, kar ka yi wasa da damar da ka samu, ka saka ta tsaneka dan Allah" Ya tsaya ya ƙarewa ƙofar gidan malam lawan kallo, yayi ƙwafa ya shiga gidan, ba tare da ya tanka Walid ba. Jiki na rawa ba tare da ta yi fushi ba, ta kawo masa tea da buredi. Ya gama baccinsa ya tashi, ya yi wanka, ya gama ya ga ta kafa masa ƙusar rataye soso a banɗakin, har zai rataye yayi tsaki ya yar da soson a kan sabulun ya fito. Ya canza kayansa ya fito falo, Satar kallonsa take yi, kamar ya ƙara kyau, kwana biyun da ya yi a tsare ba ya shan komai, kamar ya yi kyau sosai. Sai murna take yi ya dawo gida. "Ke!" Ta ɗago ta kalleshi. "Meye sunanki ne?" "Jauhar" Ya kalleta ya ce "Me? Angela?" Murmushi ta yi ta ce "Angela kamar wata mage,  sunana Jauhar" Guntun tsaki ya yi ya ce "A saka muku normal suna, sai dai a saka ƙaƙale-ƙaƙale da iyayi, ni ba zan iya ba" "To ka kirani da fatimata fatima zahra" wani irin zirrrr ya ji a jikinsa, fatima zahra, sunan mace mai girma da daraja a idonsa, Ummansa abar ƙaunarsa, duk da ba ta duniyar, amma idan ya ji sunan har wata tsuma yake yi. Ya maze ya ƙarewa falon kallo, ya fita tsakar har zai wuce ya kalli kitchen ɗin ta sannna ya ce "Zo nan" Ta fito ta ce "Gani" "Wa ki ka sayar wa carfet ɗinki da kwanukanki?" Gabanta ya yi wata irin mummunar faɗuwa, yaya aka yi ya gane ko ya sani? Sai ka ce aljani? Ya ƙare mata kallo ya ce "Ina jinki, ya aka yi ki ka samu wannan kuɗin da ki ka kai? Ina kuma abubuwam da na tambayeki? Ki ka yi mini ƙarya kuma jikinki ya gaya miki" Kamar munafuka, haka ta zayyane masa komai. Bai ce mata komai ba, ya fita. Sahura na tsakar gida, tana hira ita da wasu coustomominta, kawai ta ga wasu irin zaratan matasa su uku, a tsakiyar tsakar gida da manyan gorori kamar za su farauta. Ta tashi ta ce "Lafiya malam? Me ku ka zo yi mini a gida. Wannan ai.... Haɗiye maganar tayi, da ya sako ƙafarsa cikin isa tsakar gidan. Yana shigowa idonsa ya sauka a kan carfet ɗin, a shimfiɗe a falonta. Ya ce "Liti, ku naɗo mini carfet ɗin nan" Ta waro ido ta ce "Malam lafiya?" Walid ya zaro wuƙa ya ce "Ki ka kuma magana, sai kin ɗaware daga sararin nan yanzun nan" daga ita har sauran matan, suka hau tsuma. Kamar abun banza, suka din ga yi mata cilli da kujeru, suka naɗo carfet. Viper ya ce "Dubu sha biyu ki ka saya ko?" Ta jinjina masa kai. Ya ce "Ɗaukko mini sauran kayan da ki ka karɓa a wurinta" jiki na tsuma ta shiga ta kwaso su. Ta ajiye masa a tsakar gidan, ya ce "Ɓarauniyar zaune, daga yanzu ki san abun da zaki din ga saya, ban da a nutse na zo miki, sai na saka an zana miki awarwaro a hannu, yadda gobe ba zaki sake zalunci ba. Liti ba ta kuɗinta". Liti ya zaro kuɗi zai bata, Al'amin ya ce "Wait, ta riga ta shimfiɗa a ɗakinta, ka cire dubu uku a kai, sannan ka sake cire dubu biyu zan cika ku wanke mini carfet ɗin ku kai mini gida. Haka kuwa aka yi, suka cilla mata kuɗi, suka kwashe kaya suka tafi. Jauhar ta na yi wa wasu stone work, dan kuwa matar ta fara kawo mata kayan tana yi, hakan yana ɗebe mata kewa. Ba ta yi aune ba, ta ganshi a tsakiyar falo, hannunsa da kaya, ya dungurar mata da su a tsakiyar wurin ya ce "Daga yau, ko cokali ki ka kuma sayarwa, saboda ni sai na ɓata miki rai, fiye da yadda ki ke tunani" Baki buɗe ta ce "Master, karɓowa ka yi, kuɗinta suna wurina fa, Allah zai kaman..." "Na ba ta kuɗinta, ko tsintsiya ki ka sake sayarwa, zan gane kuma ranki sai ya ɓaci". A hankali ta ce "Na shiga uku". *** Matasa ne a ƙalla su biyar, dukkanin su, babu wanda ya gaza ko ya wuce shekaru ashirin da biyu, suna sanye da tufafi masu nuna datti, gashin kansu da yanayin fuskarsu kuwa, babu tambaya sun bayyanar da tsantsar rashin ji a tattare da su, sai bushe-bushe suke yi, suna shewa. Wani matashin ne ya diro ta saman katanga, gaba ɗaya suka nutsu, suna yi masa sannu da zuwa. "Kai gayu akwai matsala wallahi" gaba ɗaya suka tattara masa hankalinsu suna sauraren sa. Ya ce "Kaii, wai ashe mai zamani ne ya tare a unguwar nan kusan sati biyu bamu sani ba?" Ɗaya daga cikin su ya miƙe ya ce "Ƙarya ne wallahi, me yake yi mana a unguwa". "Nustu, ni ma ban sani ba sai ɗazu, mai unguwa na ji yana maganar, sai za su je police station, ko a sasanta ayi zaman lafiya da shi, ko ya bar unguwar nan". Ɗayan ya yada sigarin hannunsa ya tashi ya ce "Guduma gaskiya kar dagus ɗin ka ya janyo mana matsala, ya san waye mai dogon zamani kuwa?". "Guys mafita ɗaya ce wallahi, kun san ba a sarki biyu a zamani ɗaya ko?" "Me ka ke nufi?" Guduma ya ce "Dole ɗaya ya bi ɗaya" "To waye zai bi wani?" "Kwanciyar hankalinmu da nustuwarmu, shi ne mu yi mubayi'a, samunsa ma a unguwar nan wani security ne, zai sa a din ga jin tsoranmu" Wani matashi ya ce "Ƙarya ne wallahi, babu wanda ya isa ya zo unguwarmu mu yi masa mubayi'a ba a isa ba". "Kai Kwano, bari na yi maka wani lissafi, duk sarkin da ya zo garinka ba da ziyara ba, ya shafe awanni arba'in da takwas, a irin harƙallarmu, to ɗayan biyu, ko dai ɗaya ya bi ɗaya, ko kuma a yaƙi juna, a kama sarki ɗaya da mutanensa a matsayin ganimar yaƙi, mu rayu a matsayin bayinsa, harƙalar da Mai zamani yake yi, ta ci uban tamu, ba sa'anmu bane ba, mu yi abun da ya dace, idan kuma mu ka bari rigima ta ɓalle, wallahi a unguwar tamu, zamu rayu kamar bayi ne amma ku yi tunani". Can Al'amin kuwa yana zaune a station, ga mai unguwar da yake da sauran mutanen unguwa. Yana zaune yana kallonsu, suna ta ɓaɓatun gaskiya ya tashi ya bar musu unguwa, saboda bad record ɗin da suka samu, a kansa daga in da ya baro, kuma nan ma ya zo yana yi musu shaye-shaye kar ya ɓata musu yaran unguwa. Suka yi suka gama, yayi shiru kamar mai zancen zuci, suka yi suka gama, D.P.O ya ce "Malam Aminu, ka ji abun da mutanen unguwar da ka tare suka ce, me za ka ce?" Sai da ya ja wasu seconds, sannan ya ɗaga kai, ya kalle su da jajayen idanunsa masu matuƙar kwarjini, duk suka yi shiru, suna sauraren sa, ya ce "Haryanzu ban ji an ce ga abun da na yi ba ai. Ba zan ce komai yanzu ba, gobe in Allah ya kaimu, mu haɗu a nan ƙarfe huɗu na yamma, zan faɗi abun da na yanke". D.P.O ya ce "Ina fatan ba wata ɓarnar zaka yi ba?" "Ba na sara sai an zo ramina" daga haka bai kuma cewa komai ba, ya tashi ya fice, ba tare da ya jira iznin hakan ba. D.P.O ya ce "Abun da nake so da ku shi ne, ku bi yaron nan a sannu a samu maslaha, kar ku yi wani abu da zai tunzura shi, ya fara yi muku fitina a unguwa, ku bari mu bi a hankali mu sasanta, ɗan ƙasa ne yana da damar zama a in da yake so, ku bi a hankali ayi musu sulhu". Shi kuwa yana fita, ya kira wayar liti, bugu biyu ya ɗaga. "Liti, nan da mintuna arba'in zuwa awa ɗaya, ina son ka tattara mini, duk wasu yara marasa ji a arear unguwar nan da nake da kewayenta, duk wanda ya yi gardama, ayi masa ɗaurin igiya da swizaland gaba da baya, a layin gidana nake son su taru". Liti ya amsa da "An gama shugaba" Sahura kuwa, sai da ta je har gidan maman halimatu ta ƙare mata cin mutunci, a kan yadda Al'amin ya je har gida, ya ƙare mata tanadi, a kan ta sai kayan matarsa, maman halimatu ta din ga ba ta haƙuri, ta ce su shiga gidansa su yi magana da jauhar ɗin, amma ta ce ai ba mahaukaciya ba ce ita, da zata shigar masa gida ya ritsata ya kashe. Jauhar tana ta aikin stone, ta ji ana wata irin busa a unguwar, kamar da ƙaho ake yin busar, irin bushe-bushen da aka din ga yi, ranar ɗaurin aurenta, dan haka gabanta ya faɗi ta shiga cikin tsoro. Sannu a hankali, hayaniya ta fara cika layin nasu, da surutan matasa, ɗaki ta gudu ta rufe ƙofar falo, dan tunani ta fara yi, ko yaran madaki ne, gashi ba waya ce da ita ba, balle ta kira Al'amin Kafin ya ƙarasa layin gidan, liti ya kira shi a waya, ya sanar masa sun fara taruwa matasan, dan haka bai bi ta cikin ba ya bi ta baya. Jifff! Ta ji dirar abu a tsakar gida, ta katanga ya diro gidan, ya fara ƙoƙarin buɗe ƙofar falon, amma a rufe ya jijjiga ya jijjiga amma ya ji a rufe. Ya shiga bugun ƙofar kamar yaƙi, ƙulewa tayi a ɗaki, ta hau addu'a, tare da tunanin ta ta ta ƙare, yaran madaki sun zo neman Al'amin, ko sun zo sassarata. "Ke malama ki zo ki buɗe mini ƙofa" sai da ta ji muryarsa, sannan ta fito ta buɗe, ta kalle shi, ta leƙa tsakar gida ta ce "Ai ban san kai ba ne, biyoka aka yi ne?" Wani irin kallo ya yi mata, ya ce "Matsa ki bani wuri" ta matsa ta bi bayansa tana surutu "Master ka daina dirowa ta katanga dan Allah, gaba ɗaya na tsorata wallahi, na zata madaki ne, suka zo nemanka na ji sai busa ake yi ga warin kayan shaye-shaye...... Haɗiye maganar tayi, da ya waiwayo yana yi mata kallon warning. Ta ce "Yi haƙuri, ka ga abokanka sun dawo da carfet ɗin, wai wanke shi suka yi, amma dai yakamata na je na bawa dillaliyar nan haƙuri, ai ka ga an shiga hakkinta, har gida ta zo tayi wa maman halimatu masifar abun da ka yi" ɗakinsa ya shiga, ya kulle ƙofar ya saka sakata ya bar ta a bakin ƙofa. Sai abun ya bata dariya, kafin awa ɗaya matasan nan sun kusa cika layin nan, sai hayaniya suke yi. Malam lawan kuwa, a waya matarsa ta kira shi, ta ce kar ya kuskura ya dawo yanzu, 'yan daba sun cika layin nan. Jauhar na ɗakinta, tana aikinta, ta ji yana buɗe gate, a razane ta fito saboda yanayin bushe-bushen da ake yi, ya tabattar mata da akwai matsala. Yana fita wurin yayi tsit, kamar ba su ne suke hayaniya ba da. "Sai da kai sarki, ƙaramin dodo magajin babban, ko ma in ce ka ɗara shi. Mu na yi maka maraba da zuwa wannan unguwar, mun fito ƙwanmu da kwarkwata domin yi maka mubayi'a". Cewar guduma yana geɓare baki, yanayin yadda yake maganar kawai a buge yake. Viper ya goya hannunsa a bayansa, ya ce "Manyanku sun kai ƙarata a kan yarjejeniyar zaman lafiya, sai dai ni da ku zan yi wannan yarjejeniya. Abu goma a cire bakwai a tara da ɗaya zan gaya muku, a bi iyaye, ayi caji kaɗan saboda lafiyar jiki da ƙwaƙwalwa, a kiyayi taɓa kayan wani. Babu zubar jini a tsakanin ku, ko duk wani wanda yake unguwar nan, abu na ƙarshe mafi muhimmanci da fari salin alin na so zama a unguwar nan, wataƙila na ɗan lokaci na baku wuri, amma tun da abun ya zo da haka, sarki biyu ba zai yi sarauta a zamani ɗaya ba. Ko dai mutum ya yi mubayi'a ko ya bar unguwar nan. Kar kuma a kuskura a matsi ramina idan ba haka ba, zan yi ɓarna. Mu haɗu da shugabannin dabar Unguwar nan da kewayenta gobe a station ɗin unguwar nan, domin yarjejeniyar zaman lafiya. Kuna iya samfewa" Su ka din ga yi masa kirari, yana jin kansa yana sake fashewa. Bayan sun watse, maman halimatu ta shigo, tana ba ta labarin abun da sahura ta zo ta yi mata. Jauhar ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri maman halimatu, dan Allah ki bata haƙuri, ba yadda zan yi, na so mayar mata ma da kayan, ya ce idan na sake sayar da wani abu, zai ɓata mini rai. Wallahi yana ankare da komai, ko cokali na sayar zai gane, ni har tsoro yake bani, bari na baki dubu goma a kuɗin, ki kai mata ta ƙara ki bata haƙuri dan Allah" Maman halimatu ta ce "To shikenan, Allah ya kyauta" ta bata dubu goma ta kaiwa dillaliya, ita kuma ta bata kyautar dubu biyu, sauran kuɗin kuma ta ɗan yi musu cefane dan kuwa shi babu ruwansa. Washegari tun ƙarfe biyu, su mai unguwa suka koma police station, suna jaddada dole a kori Al'amin, dan jiya kafin su je gida ya rigasu zuwa, ya tara musu dandazon 'yan daba a unguwa. Al'amin bai je ba, sai ƙarfe huɗu tare da rakiyar su walid, da kuma matasan yara 'yan shaye-shaye da sun kai ashirin da wani abu. D.P.O ya ce "Lafiya, waɗanan fa?" Al'amin ya kalli mai unguwa, ya nuna masa guduma ya ce "Ka san wannan? Ko ba ka bani amsa ba ɗanka ne, meyasa ba ka kore shi daga unguwarka ba? Ko dan shi ɗanka ne?.  A wannan ba wannan matasan wakilai ne da suke jagorantar wasu yaran a ƙarƙashin su, wanda duk a cikin unguwarka suke, kana nufin a sati biyu da zuwana duk ni na lalata su? Har na tare a unguwar nan, ba su san waye ni ba, sai jiya da na saka a tara mini su. Dama can kuna da lallatun yara, harƙallata nake, ba na lalata ɗan kowa, duk ɗan wanda ya lalace, dama lalataccen ne. Ina sake maimaitawa ba na harbi sai an matsi ramina ko in da nake. Ga mafita zan bayar, wadda ba zan ƙara ko rage wani abu daga abun da zan faɗa ba. Mafita biyar ce ba uku, ko dai a haɗa a kore ni, da ni da yaran nan, ko kuma ku yi wa gidana kuɗi ninki uku, yadda zai isheni na sai wanda ya fishi, na bar muku unguwa, idan ba haka ba....... Ba na ƙarasa magana sai dai na aikata. Duk sai suka yi ɗif D.P.O ya ce "Mai unguwa mai ku ka yanke?" Shiru suka yi ba su ce komai ba, D.P.O ya ce "Tashi ka ja zugarka ka tafi, babu wani abu in sha Allah". Ya miƙe ya ce "Galibi yaran nan secondary school drop out ne, wasunsu idan son zuciya ne ya kai su wannan halin, wasun su laifinku ne, ko dai ku nutsu ku gyara rayuwar matasan yaran nan, ko kuma su cigaba da lalacewa kuna rusa al'ummarku da hannunku" yana gama maganar suka fice da shi da su. D.P.O. ya ce "Yaron nan fa ya san abun da yake yi, jiya kuna barin wurin nan, daga can unguwar su, Aka kira ni aka ce a gargaɗe ku, babu ruwanku da shi, yaron 'yan siyasa ne, dan Allah ku lallaɓa ku zauna lafiya da shi. Bayan sun bar station ɗin, wani irin ɓacin rai ya din ga cizon zuciyarsa, a duk lokacin da aka samu matasa ire-iren sa, al'umma ba su da wani burin da ya wuce, yin watsi da shi, da nesanta kansu da ire-iren su, bayan su ne ƙashin bayar lalacewar ta su. Yau abun na sa ya fi na kullum, domin kuwa a buge ya dawowa jauhar, wajen ƙarfe sha ɗaya na dare, ya wuce ɗakinsa, ba ta kula shi ba ta koma gefe ta zuba masa ido. Washegari da safe shiru bai fito ba, ta leƙa ɗakinsa, ta tarar da shi a kwance yana bacci, gefensa ga kwalin ashana da na taba, ga kwalabe. Shiru ta yi ta sunkuyar da kanta ƙasa, a hankali ta fara magana "Sun san da haka suka aura mini kai, Allah na roƙi ka bani mafita ka zaɓa mini shi, Allah ka kawo mini mafita, Allah ka shirya mini shi, Allah shiriya taka ce, Ni da shi duk bayinka ne, Allah bai gagari ikonka ba, Allah ka shirya min mijina. Allah ka sa ya daina abun da yake yi, Allah kar ka sa ya mutu yana saɓa maka" ta yi maganar tana kuka. A hankali ya yi juyi, satchets ɗin ƙwayoyi, suka zubo daga aljihun gaban rigarsa, ta saka hannu ta kwashe su, da kwalaben, ta hau caje ɗakinsa, duk wani nau'i na abun da ba ta yarda da shi ba, sai da kwashe daga ɗakin. A hankali ya motsa, ya buɗe idonsa, ita kuma ta fice daga ɗakin. Da ƙyar ya iya tashi, dama bayan sallar asuba, ya sake yin shaye-shayen. A yunwace, ba tare da ko wanke baki yayi ba, ya hau cin abinci, saboda kayan shaye-shayen sun rarake masa ciki, ji yaya ko tsayuwa ba zai iya yi a kan ƙafafuwansa ba, sai da ya gama ci ya dawo dai-dai. Ya shiga banɗaki, ya wanke bakinsa ya fito falo, ko ɗaga jauhar ba ta yi ba, balle ta kalleshi. Ya je gabanta ya miƙa mata hannu. Ta ɗago ta kalleshi. "Bani abun da ki ka caje mini ɗaki ki ka ɗauka" gabanta ne ya faɗi, mutumin da yake bacci ya aka yi ya san ta ɗauka?. "Bani mana" "Na zuba a shara an zubar!" (Yau juma'a mu yawaita salati, ga shugaba Sallallahu alaihi Wasallam) Ayshercool 08081012143 24 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Duk da cikin matsanancin tsoro da tashin hankali ta bashi amsar, amma ta tattaro jarumtarta ta dake, ta ƙi kallonsa. "Ai ɗago kai zaki yi ki kalle ni, ki bani amsar da ki ka faɗa yanzu" Ta yi shiru, tana jiran yayi mata duk abun da zai yi mata. Ya ce "Dama ba ni na kawo ki gidan nan ba, kuma ba ni na ce a kawo ki ba, idan kin gaji ki tafi dama kin isheni, kuma idan ki ka kuma zuwa kaina ki ka tsaya ki na kuka, sai na ɓarar da ke". Gabanta ya faɗi, a buge ta tarar da shi yana bacci, ya aka yi ya san duk abun da ya faru, sai dai kalmarsa ta ƙarshe da ya ce a kawota ba, ta yi mata ciwo. Ta zata zai yi mata tijara, da ta ce ta zubar, sai kuma ta ga ya tashi ya nufi hanyar fita, kawai ta fara kukan da ba ta san na menene ba ma. Waiwayowa ya yi yana kallon ikon Allah, da ta samu bai casata ba, da ta ɗebe masa kaya,ta ce ta watsar kuma ya san ƙarya take yi ba ta zubar ba, shi ne saboda samun wuri har da ɓare baki tana kuka. Sosai yarintarta ta fito, yadda ta tura baki tana kuka, tamkar irin 'ya'yan madarar nan shagwaɓaɓɓu. Kawai ya girgiza kai ya fice, kafin ta fusata shi. Rahila da Zakiyya kuwa sai shewa suke yi, tare da farincikin yadda shawarar da suka yanke ta yi amfani. Zakiyya ta ce "Ni fa na zata yadda yake ɗin nan, ana kaita ya korota tun da ba son auren yake yi ba, amma dama na san ko zai daketa ya cinye abu ne mai wahala ta faɗa ko tayi yaji, juriya ce da ita kamar dutse shegiya". Rahila ta ce "Shi ɗin me? A duniya akwai namijin da zai ce ba ya son mace ne, ke ban da abun makirci wannan yarinyar son kowa ƙin wanda ya rasa, wa zai ce ba ya so, dan ma ƙarama ce, gashi ai sati biyu kenan sun yi luf daga shi har ita". "Wallahi na zata ba zai saurareta ba, ƙila ma ya korota, a yadda ki ke bani labarin yadda ya zama, da kuma rashin jin da yake yi". "Ba fa mahaukaci ba ne, idan ta iya zama da yaron nan, ba lallai ki ji kansu, ai duk wannan bala'in da nake yi da tashin hankali a kansa, wasu lokutan shi da 'yar uwassa yana yi mata abu, ke har magana shahida take gaya mini a kansa" Cikin mamaki zakiyya ta ce "Kai haba dai?" "Wallafa Allah, ba suna school aka yi auren ba, sai da na kusa dukan yarinyar nan, ƙiri-ƙiri wasu lokutan take nuna in daina takurawa ɗan uwanta, aikuwa ubanta nake ci". "Gaskiya kar ki zauna a kanta, ita ana neman mafita tana shirme? Ni kam yanzu menene abun yi ne? Ƴan uwan Alhajin nan fa sun zo, wai ayi aure ayi visa ta bi shi china" Rahila ta ce "Aikuwa sai dai a lahira idan ana zuwa". "Aikuwa, wai yanzu ya fasa dawowa nan da watan ɗayan ba, ina nan dai ina ta lallaɓa uban, a kan ya haɗa shi da hafsa". "Ai ba iya lallaɓa shi ba, malamai zamu cigaba da yi, in sha Allah sai abub nan ya tabatta, ita waccan ai an gama da babinta". Zakiyya ta ce "Haka ne kam, to Ubangiji Allah ya amince, ni dai ko nawa ne zan kashe, idan ta aure shi na san zan mayar da kuɗina". "Kar ki damu ai ba zama, za ayi duk mai yiwuwa, hafsa zata auri mutumin nan". *** "Ku yanzu a ganinku ya dace mu na ji mu na gani, baƙo ya zo unguwarmu ya saka mu yi masa mubayi'a? Baƙo ne fa, mu kuma a nan aka haife mu muka girma, muka kafa sabgar nan, kuma ace sai dai mu bi shi, ba dai ya bi mu ba?" "Wallahi nima dai haka na gani, abun yayi mini ciwo, guduma ya fi kowa bani haushi shege, ai wallahi sai dai a rabu biyu, ayi ta zubar da jini, har sai ya yarda ya bi mu, ba wani shege da zai shigo arearmu ya buɗe mana ido, mu zagaya mu ji ta bakin sauran, mu ji su waye suka bi, kuma suwaye za su yi tawaye". Ɗaya matashin, ya hurar da hayaƙin wiwi ya ce "Mu tabattar da suwaye a tare da mu tukuna, zamu yi masa sara na warning, idan ma ta kama, mu kawar da shi da ga sararin nan, ba wani ɗa da zamu yi wa biyayya, tun da muka yi wa iyayenmu ma tawaye". Suka cigaba da tattaunawa a kan yadda za su ɓullowa lamarin, su yi maganin Al'amin. ***** Kamar masu kasa gyaɗa, haka suka kewaye farantin wiwi, suna naɗawa a takarda. Suka mayar da wata ƙwaya garri, suka haɗata a cikin wiwin, ita ma suka ɗaura ta daban. Matasa ne suka din ga shigowa da ɗai ɗai, suna karɓa, suna zube balance, suna karɓar kaya. Liti ya shigo cikin ɗakin da Al'amin yake, da robar abinci, ya zauna ya ce "Taso ga abinci" Ya tashi zaune ya kalli miyar kan abincin, sai ya ji ƙyanƙyamin abincin, miyar sam ba ta ji mai ba, ga ta ba ta soyu ba, ba irin wadda waccan taɓararriyar yarinyar take bashi ba. Guntun tsaki ya ja, Walid ya ce "Lafiya?". "Na ƙoshi" "Meyasa?" Ya girgiza kai ya ce "Bakomai". "Ka ce mini kawai, abincin amarya zaka je ka ci, wai mu ko sau ɗaya ba zaka kawo mana abincin na ta mu ci ba? Sai dai ka yi ta ci kai kaɗai?". Kai tsaye ya ce "Ba zan kawo ba" "To ka ƙarata, ku ci ku kaɗai, dama ni naga kamar haushina ma take ji, ban san me nayi mata ba". Ya tashi yana fatan Allah ya sa ya je ya tarar ta yi abinci. Sai kuma ya tuna kukan da tayi kan ya fito, ƙila ma ba ta yi girkin ba. Sai dai kafin ya ƙarasa gidan, aka tsuge da ruwan sama, dan haka ruwa yayi masa duka, yayi ta sauri ya ƙarasa gida, ya san ƙarshenta ruwa yau ma ya shigar mata falo. Sai dai yau aka yi sa'a, ruwan bai shiga da yawa ba, sai dai tsakar gidan ya cika da ruwa. Tana ɗakinta tana salla, ya fara cire kayan da suka jiƙe, ta shigo da sallama, sai dai cikin matsanancin hanzari, tayi wani irin burki, ta juya. Shi mamakin ta yake yi, sam ba ta da zuciya ba ta fushi. Ba tare da ta waiwayo ba ta ce "Ina da ruwan zafi a flask, na kawo maka ka yi wanka, sai ka ci abinci kar ka yi mura saboda ruwan da ya dake ka?". "Kawo" sumi-sumi kamar mara gaskiya. Ihunta ya jiyo a tsakar gida, bai san ya aka yi ba, sai ganinsa yayi a tsakar gida, cikin hanzari yana zaton wani abun ne ya sameta, tayi jifa da flask ɗin a gefe, Allah ya sa na silver ne tana ihu, ta maƙale a jikin bango. "Ke menene? Meyafaru?" "Kwaɗo ne, zai riƙe mini ƙafa" Ji yayi kamar ya ƙarasa, ya kwaɗeta, wai kwaɗo take yi wa wannan ihun. "Zaki rufe mini baki ki zo ki wuce, ko sai na zo na tumurmusa ki?" Jauhar ta ce "Tsoro nake ji wallahi" tayi maganar tana ɗagowa, idanunta har sun yi ja. Sai dai mayar da kanta ƙasa tayi, da sauri, tana tsuma saboda babu riga a jikinsa, wani irin gashi ne a jikinsa, tun daga ƙirjinsa har saman cibiyarsa. "Ke ba na son gulma, miƙo mini flsk ɗin, idan ya so ki dauwwama a wurin" Cikin shagwaɓa ta ce "Wallahi da kwaɗo a cikin ruwan nan, tsoronsa nake ji" tayi maganar idanunta na bayyanar da tsantsar tsoro da tashin hankali. Cikin ruwan ya biyo, ya zo ya ɗauki flask ɗin, zai bar kitchen ɗin ya bar ta, ta saka hannu ta riƙe masa wando, tana ihu. Sai yanzu ya leƙa ya ga kwaɗon ne da gaske, amma girmansa ba wani ƙato bane take wannan ihun, shi bai taɓa jin wai ana tsoron kwaɗo ba, sai yau. A ransa ya ce 'Laifin iyayeki ne da suka zaɓa miki wannan rayuwar' Kwaɗo ya tsalla yayi waje, ita kuma jikinta sai rawa yake yi, cike da tsoro. "To ai sai ki cikani, tun da ya tafi ko?" Cikin tsananin jin kunya, ta sake shi, ta koma gefe. "A nan wurin zaki dauwwama kenan?" Ta ce "A'a idan ruwan ya bushe, na wuce, ka duba ɗakina akwai man zafi a kan mudubi, idan ka yi wankan ka ɗan shafa kar ka yi mura, abincinka yana ɗakinka" kallonta yake yi, yana son gane nature ta ce a haka, ko kuma iya shege ne, amma yadda take ƙifta ido a tsorace ya tabattar masa da gaske take. Ba ta yi tsammani ba, ya saka hannu ɗaya ya ɗago ƙugunta, hannunsa ɗaya kuma da flask taku kaɗan yayi, ya direta a tsakiyar falo. Kallonsa take yi da mamaki, shi kuma ya nufi ɗakinsa. Har ɗan tsalle ta yi, dan ta tabattar ta na da nauyi ne, ko ba ta da shi, da ya ɗauke ta kamar wata 'yar teddy. Ta fi mintuna sha biyar tana cigaba da mamakin yadda ya ɗagata kamar a bar banza. Tuwon shinkafa ta yi da miyar taushe, kamar ya cire kunne dan daɗi, ga katifarsa ta saka sabon bedsheet, ɗakin yana ta ƙamshi, amma hakan bai hana shi goge mata hannu a jiki ba, ya gama ya miƙe yana bacci, kayan na sa ma sai ƙamshi suke yi. Leƙawa ta yi ɗakin nasa, ya mimmiƙe a kan katifa, bai saka rigar ba yana bacci ta lallaɓa ta shiga da sanɗa zata kwashe kwanukan. Yanayin garin da sanyi saboda ruwan da aka yi, amma ya takure yana bacci. Ta fitar da kwanukan, ta ɗaukko bargo daga ɗakinta, ta zo zata rufe shi, ɗan ƙura masa ido ta yi. Al'amin ba shi da wata makusa, da yake baccin nan ma he looks very innocent and calm. Kasa rufe shi ta yi, ta tafi tunanin ya aka yi ya fara shaye-shaye, ya aka yi su mama suka samo shi ma, suka aura mata? A ina yake ina ne gidansu? Duk take tambayar kanta. Tashi ya yi zaune kamar aljani ya ce "Meye ne kin zo kin sakani a gaba kina kallona" Zabura ta yi ta ce "Yi haƙuri, na zata bacci ka ke yi, ba kallonka nake yi ba, na ga kamar kana jin sanyi ne, bargo na kawo maka" tayi maganar tana tsuma. Ya miƙa mata hannu, ta bashi bargon, ya ware shi ya lulluɓa, ta fita tana mamakin al'amin idan yayi wani abun mamaki yake bata, har da ajiyar zuciya ta ji yana yi alamun baccinsa yayi nisa, amma kawai ta ganshi a zaune. *** "Allah ya taimaki maigida" "An gaisheka, ya ake ciki?" "Komai normal, ba wani abu" "Yaya za ayi? An kama Ja'afar da kaya, hukumar nan sun ƙi sakinsa, ba zan matsa ba, amma ina buƙatar a musanya shi da wani" "Oga ba zan iya sakinsa kai tsaye ba, amma dole za'a samu wani a kama shi da kayan, sai a saki jafar a kama shi, ka san wannan karon shugaban namu, yana da sanya ido sosai" "Shikenan, ayi abun da yakamata kawai" "Ok sir". Cikin ikon Allah, matar nan tela, tana biyan jauhar, duk da ba wani kuɗin kirki take bata ba, amma tana jin daɗi sosai da sosai, ta sayi katin tara kuɗi, ɗan abun da tayi cefane, sauran sai ta saka a kati, kuma Allah ya saka mata albarka a ciki. Yaran maƙwabta idan sun shigo, tayi musu tsifa da kitso, babu ko sisin iyayensu. Ta duƙufa tana aikinta, ba ta ji motsinsa ba, sai jefo mata bargo yayi a ka. A razane ta tashi, bargon kuma ya cukuikuyeta. Ya ce "Zaki taka kwaɗo" Ihu ta saka ta samu ta cire bargon da ƙyar, tana dube-dube, yana tsaye yana kallonta, kamar ba shi yayi maganar ba. Ta ce "Ina kwaɗon?" Ya yi shiru bai ce komai ba. Ta kalli yadda stone ɗin ya zube kamar ta yi kuka ta ce "Kalli yadda ka saka na zubar da kayan sana'ata." Ta durƙusa za ta kwashe, sai kuma ta yi sauri ta hau kan kujera, ta maƙale ƙafafuwanta ta ce "Ina kwaɗon ya shiga ne?" Haryanzu shi dai bai daina mamakin yadda kwaɗo ya zama abun tsoro ba. Hanyar fita ya nufa, ta gane tsokanarta yake yi, nan ta ƙara jinjinawa ƙi faɗinsa, har ya iya ya tsokaneta, amma ya sha kunu ba fara'a. "Master" ta kira shi. Ya tsaya bai waiwayo ba. "Dan Allah idan Allah ya yassare, ka taho da omo, zan yi mana wanki". Yanzu ma bai yi magana ba ya fita, ta naɗe bargonta, ta cigaba da aikinta. Zakiyya kuwa, kamar zata zare, Rahila na ta janta wuraren malamai kala-kala, yadda za su samu, Hafsa ta auri Alhaji mu'azzam da zarar ya dawo. Har sha ɗaya na dare, jauhar na aikin jera stone ɗin ta a kan gadonta, dan tun tana jin tsoron zaman gidan, har ta saba, sai da ta ji bacci yana kama idonta sosai, sannan ta tashi ta ajiye kayan, tayi wanka ta fito tana shirin kwanciya. Ji ta yi ana buɗe ƙofa, dan haka ba ta damu ba, ta san mai gidan ne, sai dai bayan wasu mintuna ta ji kamar yayi jifa da wani abu a falo, yana ta haki mai kama da kakari, gabanta ya faɗi ta fito da sauri, ta tarar da shi ya riƙe hannunsa yana ta nishi, hannunsa an yanke shi, da ƙafarsa ta hagu, kasancewar da wuta, ya sanya ta ga yadda yake zubar da jini, a gigice ta ƙaraso cikin matsanancin tashin hankali ta ce "Master faɗa ku ka yi da wani? Ya aka yi ka ji ciwo haka?" Yayi shiru yana fesar da iska daga bakinsa. Da gudu ta shiga ɗakinta, ta ɗaukko zani ta danne masa na hannunsa da ya fi zubar da jini, ta rikice ta rasa me za ta yi, kawai ta nufi hanyar fita. Ya ce "Ina zaki?" Cikin tashin hankali ta ce "Maƙota zan je, a samo abun hawa a kai ka asibiti kar jininka ya ƙare". "A haka kuma zaki fita?" Sai a lokacin ta ga, ko hijjabi babu a jikinta, ta koma ɗaki, ta ɗaukko hijjabinta sai kuka take yi, tana dawowa falon ya ce "Kar ki fita" "Meyasa? Jini fa ka ke zubarwa" Ya ce "Ki ƙyale ni, zai daina zuba ne" Cikin kuka ta ce "Ni dai dan Allah ƙyale ni, sai wani abun ya same ka, idan jininka ya ƙare fa mutuwa zaka yi" ba ta ma jira me zai ce ba, ta kasa da gudu, tayi waje. Ta din ga buga gidan maman halimatu, malam lawan ya buɗe, ya tsaya yana tambayarta menene?". "Dan Allah baban su halimatu, ka taimaka mini, na ga kana da babur, mijina ne aka sare shi dan Allah a kai shi asibiti, sai zubar da jini yake yi" Ya waro ido ya ce "A daren nan, haka kurum garin taimakonku, wani abun ya same ni, shi ma idan ya samu wani haka zai yi masa, sai da safe" ya rufe ƙofarsa. Haka ta din ga buga gidajen layin nan, na ƙarshe ne mai gidan ya biyota, sai dai ba shi da abun hawa, suka zo ya tsaya a ƙofar gidan, ta shiga ciki. Yana zaune, ya kashingiɗa ya lumshe idonsa, yana jin yadda raɗaɗi yake ratsa wurin saran. "Master, taso mu je" Bai buɗe idonsa ba ya ce "Ina?". "Wai meyasa ka ke haka, asibiti mana" tayi maganar hawaye na ta ambaliya a fuskarta. Ya miƙe yayi waje, ya tarar da maƙwabcin na su a tsaye, suka gaisa Al'amin ya ce "Malam ka rabu da ita dan Allah, ka je ka kwanta, ba wani abu in sha Allah" Ya ce "A'a ga jini kana ta zubarwa, ni bani da abun hawa, na kira wani ƙanina, a nan titi chemist ɗin sa yake, ko taimakon gaggawa sai a baka" Tayi farat ta ce "Yauwwa mun gode Allah ya saka da alkhairi" Haka suka tafi, ya kira ƙanin nasa, ya buɗe chemist ɗin babban wuri ne sosai. Ya fara yi masa ɗinki, saboda raunin na hannunsa yayi zurfi sosai da sosai. Sai dai shi da ake ɗinkewa kamar ƙwarya ko a jikinsa, ita kuwa sai uban kuka take yi, tana yi masa sannu. Kawai bin ta yake yi da ido, har mamaki yake yi, yadda take nuna matuƙar damuwarta a kansa. Mai Chemist ɗin ya ce "Dan Allah ki daina kukan nan, ba wani abu, ba ki ga shi jarumi bane?" "To jininsa ba zai ƙare ba, ya zubar da jini sosai tun a gida" Ya ce "Ba zai ƙare ba in sha Allah, idan ma ya ƙare sai mu saka masa naki". "Ki daina yi mini surutu a ka kin cika mini kunne" yayi maganar a ƙule. Haushi ne ya cika masa rai, kamar ya kife mai chemist ɗin da mari. Ta ce "To na daina sannu" tayi maganar cikin kulawa. A ka gama ɗinki, ya ce zai ɗan saka masa ruwa, saboda ya taimaka masa ya zubar da jini sosai, amma fafur ya ce ba ya so. Ya haɗa masa magunguna, ya ce ya din ga zuwa ana wanke ciwon, jauhar ta ce "Sai dai ka bani kayan dressing ɗin, ba zai din ga zuwa ba". Mai chemist ɗin yayi dariya, ya haɗa ya bata, ta ce "Nawa ne kuɗin maganin? Da abun da aka yi masa?". Maƙwabcin ya ce "A'a kar ki damu, Allah ya bashi lafiya, ni zan biya". Jauhar sai da ta risuna, ta din ga yi masa godiya, sannan ta ce "Tashi mu tafi" ya miƙe tsam ta bi bayansa. Suka baro maƙwabcin na su a can, suka nufi gida. "Sannu, ka na jin jiri ne? Idan kana jin jiri mu tsaya ka huta, ko ka dafa ni" kallonta ya yi ya ga me zai dafa. Ya dai yi shiru bai yi magana ba. Suka isa gida, ya shiga ɗaki ya zauna, ta fito ta hau aikin wurin da ya ɓata da jini, dan a buɗe su ka bar gidan ma. Ya zauna ya ci abincin da ya tarar a ɗakinsa, ta ga ledar omo ce da sabulu da ta ce ya sayo, su yayi wurgi da su. Ta dawo ɗakinsa, ta tarar ya jingina ya lumshe ido, "Sannu master, yana yi maka zafi ne? Ga magungunan nan ka sha kan ka yi baccin". Ya girgiza mata kai alamar ta ƙyale shi, gumi ya fara tsatstsafo masa, saboda allurar ta sake shi, zafi ya fara ratsa shi. Saboda kar ta takura masa da surutu, ya kwanta ya hau baccin ƙarya. Ta fita ta ɗaukko mafici ta dawo, ta zauna a gefensa, ta hau yi masa firfita. Sai dai lokacin kusan ƙarfe biyu ne na dare, ta din ga zabga hamma, yana kallonta, har bacci ya ci ƙarfinta, ta saki maficin. Ya buɗe idonsa fes a kanta, har mamaki take bashi, yadda take nuna matuƙar damuwarta a kansa, kuma komai zai yi mata ba ta jin haushi. Hakazalika bai daina mamakin yadda aka yi, iyayenta suka yarda suka aura masa ita ba. Ya ciro wayarsa a aljihunsa, ya kira walid, uku sauran nan, ya ɗaga. "Walid" "Maza, ya aka yi ne?". "Ka san akuyancin da yaran nan suka yi mini?" Walid ya ce "Wane yaran, suwaye?". "Na baro chamber, na shigo cikin unguwa, kawai na ji sara a hannuna, sun kai su bakwai, suka hau ni da sara, kasheni suka so yi" Walid ya zabga ashar ya ce "Suwaye?". "Bari na yi wa ɗaya shaida, haryanzu ba su san waye ni ba, na karya biyu, sauran sun gudu, sun yi mini rauni a hannuna da ƙafata". "Yanzu kana ina?" "Ina gida, ni wallahi yarinyar nan ta fara takura mini, komai kuka, duk ta tashi hankalinta, iyayenta ba su yi mata adalci ba, ni fa ba zata hana ni rayuwata yadda nake so ba". Walid ya ƙyalƙyale da dariya ya ce "Mai dogon zamani, da uban waye ya damu da ka ji koma menene mana, tana da tausayi ne kawai da alama, ka dai daina yi mata muzurai da zare ido kawai" Yayi tsaki ya ce "Ka saka liti ya nemo mini suwaye yaran nan" "Shikenan, zamu faso gobe in ga jikin naka, sai da safe". Ya ajiye wayar ya kalli fuskarta, tana ta bacci a zaune. Hannunsa ɗaya ya saka, ya janyota ta kwanta a kan katifar, shi kuma ya jingina da bango ya cigaba da bacci. Kasancewar ba salla za ta yi ba period take yi ya sanya, tana ji ana kiran sallar asuba, ta cigaba da baccinta, sam ta manta a ina take. Ƙaurin da ya isheta ne, ya sanya ta fara tari, tayi juyi ta buɗe ido, da fuskarsa ta fara tozali, yana busa sigari. Ta tashi tana kallon ɗakin, sai yanzu ta tuna ta shigo tana yi masa fifita. Ta hau soshe-soshen cizon sauro. Ƙura masa ido ta yi, ya kawar da kansa gefe. A raunane ta ce "Master" Idonsa ya ɗago ya kalleta. "Dan Allah ka daina, ba na so zuciyata ba ta yi mini daɗi, kuma zaka cutar da kanka, kalli yadda ka je aka yi maka rauni, ka zubar da jini, haba master manya ba sa haka" tsuke bakinsa yayi yana sakin hayaƙin, a ƙoƙarin sa na hana maganganun ta yin tasiri a zuciyarsa. Ta girgiza kai ta ce "Shikenan, ya jikin?". Yayi mata banza, ya cigaba da busa sigari. "Dan Allah ko ba zaka daina ba, ka rage mana, lafiyar ka fa". "Ke, ki koma in da ki ka fito mana, ko na ɗaure ki na ce ki zauna ne? Tashi ki bar mini ɗaki". Ta gyaɗa kai ta ce "Abun har da gori, Allah ya baka haƙuri" ta miƙe idonta fal hawaye. Tana kitchen tana aikin karin kumallo, aka buga ƙofa, ta saka hijjabi ta buɗe ƙofar, ta ga walid d wasu matsa su biyu, suka gaisa suka ce mata, wurin mak dogon zamani suk zo. Ta haɗe rai ta ce "Sunan shi Al'amin, bari na yi masa magana". Tana shiga ta tarar da shi a falo ya fito. Ta ce "Ka zauna sai su shigo su ganka, amma ka ga da rauni a jikinka" tayi maganar tana sunkuyar da kai, tana jiran ya gaya mata baƙar magana. Idonta ya ɗan yi ja, saboda kukan da ta yi. Ya nemi wuri ya zauna, ba tayi tunanin zai yadda da hakan ba. Ta je ta leƙa ta ce musu su shigo. A falo suka tarar da shi, gida sai ƙamshi yake yi, gashi dai ba wani haɗaɗen gida ba, amma ta gyare gidan tsaf. Suka zauna a falo, Walid ya ce "Maza wallahi ka more, mu ma Allah ya tsamo mu, dan Allah ji wani ƙamshi kamar a gidan masu kuɗi". "Duba ni ka zo yi, ko munafunci ka zo yi?" Walid ya ce "Duka, amma dai ya jikin? Kut ka sha ɗinki kamar ƙwarya, za su ci ubansu yaran nan, kan yamma an gano su in sha Allah". Suna ta zuba, tana jiyo shi yana saka baki sama-sama, da ita ce dai ba zai yi hira ba, amma yana magana. Tayi sallama suka amsa, ta zo ta ajiye musu kofuna, da cokula da flask ɗin shayi, ta koma ta kawo jallof ɗin taliya a faranti, sai ƙamshi take yi. Liti ya ce "Allahu Akbar, sannu amarya, wannan hidima haka? Ai da mun sani tuntuni mun zo" Al'amin kallonta yake yi, da jinjinawa ƙarfin halinta, har ta ƙar sanwa, ta yi girki da su. Suka kewaye, suka din ga cin taliyar nan, liti ya ce "Kalarta kalar girkinta, abincinta mai daɗi, ita kuma 'yar beauty, wallahi maza ka more, ga gida mai ƙamshi" Ji yayi ya kasa haɗiye abincin, maimakon ya ji daɗin yabon suka yi mata, sai ya tsuke fuska ya tsame hannunsa daga kwanon abincin. Har suka gama santin, bai sake cewa komai ba, Walid kuma yana ankare da shi, dan haka da gayya, ya cigaba da kunna shi, suka gama abun da za su yi, suka fita tsakar gida suka din ga yi mata godiya. Walid ya ce "Wai ba zaka fito ka raka mu ba?" Tayi farat ta ce "A'a ba shi da lafiya ai" Walid ya ce "Au, to Allah ya baku haƙuri, Allah ya ƙara afuwa ya bar ƙauna". Bayan fitarsu ta kwashe kwanukan, ta wanke, tana ta aikinta, yana kan doguwar kujera a kwance, sai dai ba ta kula shi ba. Kusan kwanaki uku, jikin master yayi kyau, ba shi da ƙan jiki, ba zai sha magani ba sai ya ga dama, dressing kuwa cewa yayi ba ya so. A kwanakin nan jauhar na jin ciwon kai, da ciwon jiki, sai dai ba ta wani damu ba. Duk yadda ta so hana master fita, da 'yan dabaru sai da ya saka ƙafa ya fice, ya tafi nasa garari. Cin abinci ne yake dawo shi, ko sau ɗaya bai tambayi yadda take samun yin cefane ba, sai da ya zo ya ci. Tun da ya dawo gidan ya ji shiru bai ji motsinta ba, kuma bai ga abinci ba, sama da awa guda, saɓanin da, da ya shigo za ta fito. Kasa kwanciya hankalinsa yayi, ya nufi ɗakinta. A kwance take a kan gadonta, amma bai tabattar da idonta biyu ko bacci take yi ba. Ya ƙarasa gaban gadon, sai dai ya manta sunanta, Fatima zahra kuma yayi masa nauyin da ba zai iya faɗa a bakinsa ba. Ayshercool 08081012143 25 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Dukan gefen katifar da take kai yayi, amma ba ta motsa ba, ya zura kai ya leƙa fuskarta, ya ga bacci take yi. Duk da bai saba zuwa ya tarar da ita tana bacci ba. Ficewa ya yi, ya bar ɗakin, shi babban takaicin sa, rashin samun abun da zai ci. Jauhar kuwa, tun dare ta kwana ta na fama da matsanancin ciwon mara, ga ulcer ta tayar mata, sai gudawa take fama da tashin zuciya, ta samu ya lafa mata, ta kwanta ta hau bacci ga gidan yau babu abun da za ta dafa, ɗan kuɗin hannunta sam ba su da yawa. Ƙarshe dai buredi ya fita ya samo, ya dawo ya zauna a falo yana ci. Wayarsa ce ta fara ringing, ya duba ya ga kiran indabo ne, kallon wayar ya cigaba da yi, yana cin buredinsa, sai da ta kusa katsewa ya ɗaga ya saka a kunnensa, yayi shiru. "Aminu" "Mmm" "Na dawo, kai nake jira, haryanzu ba ka zo ba" "Zan zo" "Yaushe kenan? Haba kai kuwa dan Allah, ba ka san kiran me nake yi maka ba fa" Al'amin ya ce "Na ce zan zo ai" "To shikenan, Allah ya kawo ka" Ya ajiye wayar, gaba ɗaya haushin buredin da yake ci ma yake ji, sam ba ya yi masa daɗi, har aka yi kiran la'asar, ba ta fito ba. Ya tashi yayi salla, ya fito falo ya sake zama, sai ga ta ta fito tana ɗan yamutsa fuska. Fuskar duk ta ɗan ɗaga tayi jawur. Ta zo ta nemi wuri ta kwanta, ba tare da ta ce masa komai ba. "Wai yau ba abinci ne?" Yayi maganar yana wani basarwa. Maimakon ta ce masa babu abun da za ta dafa ne, sai ta ce masa "Ba na jin daɗi ne" Ya taɓe baki, ya tashi ya saka takalmansa ya fice daga gidan, fitarsa ba kaɗan, ta ji horn da tsayuwar mota a ƙofar gidan, mintuna kaɗan ta ji ana bugun gate, ta saka hijjabi ta je ta buɗe. Baba ta gani a tsaye, cikin matsananciyar murna ta ce "Baba" yayi murmushi ta ba shi hanya ya shigo. Suka isa har falonta, ya samu wuri ya zauna ta ce "Baba meyasa baka kuma zuwa ba?" Tayi maganar hawaye na cika mata ido. Wani irin matsanancin tausayinta ya kama shi, har ya ji kamar shi ma ya yi kukan, amma ya danne ya ce "To ba gani na zo ba, Waliyiyya 'yar baba" "Baba babu wanda ya zo mini, sai yaya saifu da Anty lubabatu, kowa yaƙi zuwa in da nake, wai ba za su zo ba, mijina ɗan daba ne, kuma ba abun da zai yi musu, ba ruwan shi da su. Baba ya ce "Waliyiyya, ki daina saka irin wannan abubuwan a ranki, kar su dameki, ki yi haƙuri ke mai haƙuri ce, amma ki ƙara. Ya gidan ya mijin naki?" Cikin jin kunya ta ce "Yana nan lafiya, yanzun nan ya fita" "Jauhar, ina fatan dai babu wata matsala dai ko?" Ta girgiza kai ta ce "Babu". Turus yayi ganin takalma a ƙofar falo, amma ya ƙarasa ya shiga, ba tare da ya yi sallama ba. Kallo ɗaya ya yi wa mutumin, ya ga yana yanayi da jauhar ya ƙarasa cikin falon, hannunsa riƙe da baƙar leda. Durƙusawa yayi har ƙasa ya ce wa Baba "Ina wuni" hakan ba ƙaramin daɗi ya yi wa jauhar ba, dan tun da ta ji motsin shigowar sa, take fatan Allah ya sa kar ya yi wa baba wani abun na rashin ɗa'a. Baba ya ƙare masa kallo, kai ba ka ve mara ji bane ba, dan a cikin nutsuwarsa yake, ya ce "Lafiya ƙalau malam Aminu, yau dai Allah ya yi mun haɗu, ya gidan ya iyalin naka" Ya amsa da "Lafiya ƙalau". "To masha Allah, Ubangiji Allah ya yi muku albarka, ayi ta haƙuri, ka san ita rayuwar aure, zama da mace sai haƙuri, dole za ku saɓawa juna, ayi ta haƙuri. Ba yabon kai ba, na san Waliyiyya yarinyar kirki ce, amma duk da haka na san dole wataran a saɓa Allah ya yi muku albarka" Ya amsa da Amin, ya tashi ya bar wurin ya tafi ɗakinsa. Ta ce "Baba bari na dafa maka abinci"  ta faɗi hakan, dan kar baba ya fahimta wani abu. Baba ya ce "A'a, zuwa na yi dama na ganki, ni da ba a san da zuwana ba" Jauhar ta ce "Dan Allah baba ka tsaya" Ya ce "Gidanku ba zan tsaya ba, kira mini mijinki, zamu yi magana" Ta tashi ta shiga ɗakinsa, ta ce "Master, baba yana son ganinka". Ya jinjina mata kai, ya tashi ya fito, ya samu wuri a ƙasa ya zauna. Baba ya ce "Malam Aminu dan Allah alfarma zan nema, ka san jauhar ba ta kammala sakandare ba, an fara registration ɗin WAEC ne, shi ne na ce ina neman alfarma, zan biya mata tayi registration ta yi jarrabawa dan Allah". Aminu ya ce "Babu damuwa, Allah ya bada sa'a". "Amin Aminullahi, Allah ya saka da alkhairi" Baba ya miƙe ya ce zai tafi. Cikin rauni ta ce "Baba daga zuwanka sai tafiya kuma?". "To Waliyiyya ba dai na ganki ba". Kamar mara gaskiya, haka ta biyo bayan baba, a tsakar gida ya tsaya ya kalleta ya ce "Jauhar menene?" Ta girgiza masa kai alamar bakomai. Ya juya zai buɗe gate, ta riƙe rigarsa ta fashe da kuka. Ya ce "Subhanallah, gaya mini menene? Wani abun yake yi miki?" Girgiza masa kai ta sake yi. Ta cukuikuye rigarsa, ta cigaba da sheshsheƙar kuka, shafa kanta ya dinga yi sai dai ya kasa hanata cigaba da kukan. Sai ma hannu da ya sa, yana goge hawayen da suke ƙoƙarin zubo masa, ya san ba zata faɗa masa koma menene ba, amma yanayinta ya nuna masa tana da damuwa. Dan kanta ta cika masa riga, ta goge hawayenta ta ce "Ka gaida gida baba, ka ce ina gaida su mama da Anty da kowa da kowa" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Za su ji in sha Allah, gashi ke ba waya ba, ranar talata ki je ki samu malam Hadi, a office ɗin su, zaki yi thumb print, yayi miki registration" Ta ce "To baba, na gode sosai, Allah ya saka da alkhairi" ya fita ta rufe gate ɗin, ta jingina da jikin gate ɗin, hawaye na cigaba da zuba daga idonta. Duk yadda suka yi, Al'amin yana kallonsu ta window, ta goge hawayenta kafin ta dawo ɗakin, ya bar falon. Haka ta koma bedroom ɗin ta, ta kwanta tana ta tunani daban-daban a cikin zuciyarta. **** 'yan uwan Alhaji mu'azzam kuwa, ba su gaya masa cewar an aurar da jauhar ba, suka ce masa babanta ya ce yayi haƙuri idan ya dawo ayi auren, abun ya bashi mamaki, ga wata irin kewar yarinyar da yake yi, yana jin son ta sosai da sosai a ransa, ya din ga addu'a da fatan Allah ya sa ba wani abun ne zai faru ba, saboda jinkirin da ake samu ba. Kusan kwanaki biyu kenan, jauhar bayan ta gama ciwon mara, ta koma zazzaɓi, gashi babu abincin kirki, kuɗin da take tarawa a kati, ba ta son ta je ta ce a bata, a fuskanci akwai matsala, hakan kamar tonon asiri ne ga mijinta, 'yan unguwa su samu abun faɗa. Haka zata fita ya sayo gari, da gyaɗa ko suga babu ta sha, shi kuwa garujen ko a jikinsa, sai dai yana ankare da yanayin jikinta. Al'amin na zaune a katafaren falon honorable Indabo, yana jiransa. Babu jimawa ya iso falon, yana ganinsa yayi murmushi ya ce "Ango ka sha ƙamshi, da alama amarya ce ta ɓoye mana kai har haka" Shiru yayi, ya saka babban yatsansa yana sosa girarsa. Indabo ya zauna ya ce "Tun shekaranjiya na shigo, nake nemanka amma ka ƙi zuwa. Da farko dai ina yi maka murnar angwancewa da ka yi, ina Abuja aka sanar da ni an kama ka, ana gobe ɗaurin aure, na tura P.A . Allah ya sanya alkhairi ya baku zaman lafiya" "Amin" ya amsa a ciki kamar an yi masa dole. "To yaya shirye-shirye? Ina fatan kana ƙara shirya mini yaranka, babban zaɓe yana gabatowa, idan aka yi nasara aka samu kujerar nan, Aminu zaku warwasa daga kai har yaranka, har da na kusa da ku ma, dan Allah kar ka bani kunya, duk da ba ka saba bani ɗin ba". "To" ya amsa yana kallon wani wurin daban. "Ka san meyasa na kira ka?" "A'a" "Akwai wani matashi, yana nan a social media, ba shi da wani aiki da ya wuce adawa da ni, da aibata mana jam'iyya,kuma hankalin matasa ya fara komawa kansa, na rasa yadda zan yi da yaron nan, duk wasu hanyoyi da zan bi a siyasance, na yi amma ya ƙi ganewa". "Me ka ke so ayi?". Ya jefowa Al'amin hoton matashin, an rubuta adress ɗin sa a jiki. Kallo ɗaya ya yi wa hoton, ba tare da ya ɗauka ba, ya ce "Me ka ke so ayi masa?" "Ire-iren sa suna da yawa, amma sonake ayi musu misali a kansa. Ina son yayi ido biyu da Switzerland ɗin ka, ka yi masa shaida alamar kun haɗu". Wani irin murmushi ya yi, ya fito da dogon harshen sa, ya lashi laɓaɓɓansa na ƙasa da suka yi duhu ya ce "Switzerland. Kamar ka ce idan aka samu kujerar nan, zamu warwasa da yarana da na kusa da ni, alƙawari ne ko zance?" "Wace irin magana ka ke haka ne, ba zance bane ba, da gaske nake yi mana". Al'amin ya ce "In ɗauke shi a matsayin alƙawari dai" Indabo ya yi turus, ya kasa bashi amsa. "Ba zan tura mota, ta tashi a bule ni da hayaƙi ba, ba senator ba wallahi ko shugaban ƙasa ka zama, ba za a bule ni da hayaƙi ba, dan haka maganar nan a matsayin alƙawari na ɗauketa" "Kai fa matsalarka kenan Aminu". "Menene sallamar aikina?" "Masu kauri ne, ga wannan ka fara rage ta" yayi maganar yana ajiye masa envelopes. "Ka san dai in da ka tura ni ko? Wallahi idan ka bani abun da bai yi mini ba, ba zan yi ba" Indabo yayi murmushi ya ce "Ai somin taɓi na baka, akwai ciko" Ya miƙe tsaye ya ɗauki envelope ɗin sa ya fice. Sai da ya je can dabar su, ya sallame su, sannan ya nufi gida. Da ya je gidan a buɗe ya tarar da ƙofar gidan, kai tsaye ya shiga ya tarar duk ta cika igiya da kayansa, ta wanke masa su. Mamakin jauhar yake, rashin sanin ciwon kai ne, ko me yake damunta, ta ce ba ta da lafiya, amma ta zage ta yi masa wanki, hatta ɗakinsa da ya bari kaca-kaca ta gyara masa. Ya samu wuri ya zauna a kan kujera, ya kunna sigari yana sha. Sallamarta ya ji a tsakar gida, bai amsa ba ya cigaba da shan sigarinsa. A hankali take takawa, ga yunwa ga ciwo, ta shigo hannunta riƙe da 'yar leda. Ta zauna a kan carfet jiki a sanyaye ta ce "Ka yi haƙuri, baka nan ne ban tambayeka ba na fita, magani na je chemist ɗin bakin titi na sayo" Sai da yayi wani munafukin tari, saboda tun ranar da mai chemist ɗin nan yayi masa ɗinki, ya din ga jan ta da hira, ya ji ya tsane shi, amma ya fuske yayi mata shiru. "Kar ka ga ban yi girki ba tun jiya, kuɗin hannuna ne suka ƙare, amma ga gurasa na taho mana da ita daga titi" ƙara yawan hayaƙin da yake fitarwa daga bakinsa yayi, ba tare da ya ko kalleta ba. Jin ba shi da niyyar kulata, ya sanya ta yinƙura za ta tashi, sai dai ta yi wani irin razanannen ihu, kallonta yayi da sauri, ya ga ihun me take yi, dan ya san ba zai wuce wani abun haushin ne ba, dan kamar gyare haka take da ihu. Ashe ƙadangare ne a ƙarƙashin kujerar da ta zauna a gabanta, tun shigowarsa ya ganshi, amma bai damu ba, ƙadangaren na ta neman hanyar fita, jikinsa yayi baƙi sosai, kamar an ciro shi daga kwata, yayi ba kyan gani. Tuni ta suma a wurin, dan kuwa hannunta ta ɗora a kansa ba ta sani ba. Maimakon ya tashi, sai ya zuba mata ido, cikin takaici, abu kaɗan sai ta suma, ko ta hau ihu. Kamar ba zai tashi ba, sai kuma ya miƙe. Ya saka hannu ya ɗauketa ya kwantar da ita a kan kujera, sai dai jikinta ya yi zafi sosai, sai yanzu yake tunanin zazzaɓi take yi kenan?. Ya duba ledar magungunan da ta sayo, maganin ɗaya mai hoton sauro, ɗaya kuma pcm ne. Ya kama gefen hannunta, ya ji bugun zuciyar ta yana bugawa da sauri, ya saki hannun nata yana kallonta, ita a rayuwata komai ma tsoro yake ba ta kenan. A hankali ta fara motsawa, ta yinƙura za ta tashi, ya ce "Koma ki kwanta" ta ɗaga idonta a hankali ta kalleshi. "Tsoro nake ji" ta faɗa muryarta na rawa cikin tsoro. Ya sake kama hannunta, yana jin bugun zuciyar ta, ya saki ya ce "Tashi" ta yinƙura ta tashi a hankali, kanta na sara mata ga jiri saboda yunwar da take ji. Tana daga kan kujerar a kwance, ya ɗage ɗaya kujerar da ƙadangaren yake ƙarƙashin ta, kawai ya saka hannu ya danƙi ƙadangaren ya jefa shi waje. "Na shiga uku master, ƙadangaren ka ke kamawa da hannunka" Tsaki yayi, ya wuce ɗakinsa, jikinta ya din ga rawa, tsigar jikinta ta din ga tashi. Ya dawo ya dire mata leda, ya ce "Ki ci ki sha magani" ya jefa mata wani kwali sannan ya fita. Kwalin ne ya fara ɗaukar hankalinta, ta ɗauka da sauri tana dubawa, sabuwar mp ce kar 'yar ƙarama mai kyau. Ba ta san lokacin da ta yi murmushi ba, ta hau kukkunata tana dubawa, sai da ta gama, ta ajiye ta buɗe ledar. Irin meatpie ɗin nan ne oasis manya kusan biyar, da ƙatuwar robar fura da nono. Kasancewar a yunwace take kuwa ta hau ci, ta ji babu daɗi kwana biyu tana ciwo, amma bai iya yi mata sannu ba, dama magani ba ta saka ran ya saya mata ba, mutumin da bai ba ta abinci ba wane magani zai bata, ashe yana sane, sannu ce ko ya jiki ba zai iya ce mata ba. Sai dai da tuna yadda ya ɗauki ƙadangare da hannunsa, sai tsigar jikinta ta tashi. Ana yin sallar isha'i ya dawo, mp ɗin ta har da fitila. Ta tashi tana yi masa sannu da zuwa, ya wani maze ya bata wata ledar, sannan ya zauna ya ce "Ki nemi wata ma'aikaciyar idan akwai a nan kusa, tayi miki, idan ki ka je wurin wancan ɗan iskan na bakin hanya kuma ni da ke ne" Ta saka hannu biyu ta karɓa, allurar zazzaɓi ce mai tsada ya sayo ya kawo mata, amma bai iya cewa ya jiki ba. "To godiya nake master, Allah ya ƙara arziki ya sa a fi haka, na ga saƙo ma na gode sosai da sosai Allah ya sa afi haka". "Amin". Ta ce "Ga naka na ajiye maka" Ya ce "Idan zan ci ba sai kin ce na ci ba, ki daina kuma wannan mugun tsoron, komai ya baki tsoro, idan ba haka ba ki kashe kanki a banza" Jauhar ta rausayar da kai ta ce "Nima ban san ina jin tsoron ba ne. Amma kai ba ka jin tsoron sa ka riƙe shi da hannu?" "Ban sani ba? Rannan kwaɗo yau ƙadangare, meye abun tsoro a jikinsu, har da suma saboda ƙadangare" tayi shiru ta sunkuyar da kai. Sai da ya gama sannan ta ce "Ka yi haƙuri to, ban san ya ake yi nake jin tsoron ba". "Idan ma kina sane ki cigaba da yi mini ihu a gida kamar gyare". Sai da ta yi murmushi ta ce "Zan koyi jarumta, zan daina jin tsoro in sha Allah. Yauwwa master yaushe zamu je ka kai ni na gaida su mama? Ba su taɓa ganina ba, ban taɓa ganinsu ba, su hajiya kawai na taɓa gani, yakamata ka kaini na gaishe su. Sai ayi girki mu je mu gaishe su, na ga haka ake yi". Shiru yayi, yana tuna Ummansa, tana yawan cewa Allah ya raya mini babana na ga aurenka, in ga mai sa'ar da zata auri ɗan autan mazana Jauhar ta ce "Ka yi haƙuri idan na ɓata maka rai ne maganar da na yi" Ya tashi tsam ya ce "Yauwwa, Ina sake jaddada miki, idan ba zaki iya zama ba, ko kin gaji zaki iya komawa gida, babu takura, na ga shekaranjiya kina ta koke-koke, idan da takura you are free to go" daga haka ya nufi ɗakinsa. Gabanta ya faɗi ta fara tunanin, me ta ce da zai ɓata masa rai har haka?. Haka nan ta ji ba ta fatan abun da zai sake mayar da ita gida yanzu, da sunan zawarci ko ace ta kasa zama, saboda ta san dama mugunta ce ta saka aka aura mata shi. A ranta ta ce 'Zan jure, in sha Allah zan bawa mara ɗa kunya, in sha Allah, Allah ba zai kunyata ni ba, ba zan tagayyara ba" Lokaci-lokaci yake leƙowa falo, sai ya hangota tana aikin stone ɗin ta, tana jin radio a mp. Yana so yayi mata maganar ta je ayi mata allura, amma ya fasa. Bacci ta fara, ji ta tafi ta je ta kwanta, har ta fara bacci aka kawo wuta, hasken lantarki ya hasketa, ba shiri ta tashi, sai a yanzu ta tuna ba ta kashe ƙwayayen ba, ta fita falo dan ta kashe, taga Al'amin ya fito daga ɗakinsa, yana soke wuƙa a ƙugunsa. Ta tsura masa ido tana kallonsa, bai san tana falon ba, yana ɗaga ido, suka yi ido huɗu, ɗaure fuska yayi ya zo zai fice. Ta ce "Master ina zaka je a daren nan, kuma?" Ai ko sake kallonta bai yi ba, ya nufi ƙofar fita. "Dan Allah kar ka je in da za a illataka, zuciyata ba ta yi mini daɗi in ga kana zubar da jini". Bai tsaya ba, sai da ya dangana da tsakar gida, ya kama katanga ya dira, ita kuma ta zauna a wurin ta fashe da kuka mai taɓa zuciya. Ko da ya fita titi, liti ya zo a kan babur ya ɗauke shi, suka tafi. Unguwar shiru, kowa ya shige gida, suka maƙale a wani wuri su na shaye-shaye. Can sai ga wanda suke hari, ya kwararo layin a kan babur, Al'amin ne ya fita da sauri, ya daki tayar gaban babur ɗin, aikuwa ya faɗi ƙasa da shi da babur ɗin. Suka rirriƙe shi, Al'amin ya zagaya dai-dai kunnensa ya ce "Tijjani Faruk ko? Gargaɗi aka ce ayi maka, a kan rubuce-rubucen da ka ke yi a dandalin sa da zumunta, da waɗanda ka ke suka, da Switzerland na so na yi maka warning ɗin, amma a yadda ka ke ɗin nan, zaka iya ɗayewa idan nayi maka da ita, ko iraƙi na saka maka a jiki ba zaka shura ba. Liti, duba bayana, ka ciro Russia ka yi masa rijiya a cinya, ka yi masa eleven da iraƙi a gadon bayansa". Tijjani yana ihu, yana kururuwa, yana komai, liti ya caka masa wuƙa a cinyarsa, ya yage masa riga, ya yanke shi sau biyu a baya, ya watsar da shi a wurin yana kururuwa. Can gida mama tana ta sintiri, har sha biyu saura, ba ta ji an ce Tijjani ya shigo gida ya ɗauki abinci ba, ta din ga kiran lambar wayarsa amma a kashe. Tana ta mita, aka kira baba a waya, aka sanar musu, an tsinto tijjani a hanyar dawowa gida, an yanke shi da makami, an tafi kai shi asibitin cikin gari, sashen bayar da agajin gaggawa. Ɗora hannu ta yi a ka, tana ihu tana ta shiga uku an kashe mata ɗa. Baba ya ce 'Ba cewa aka yi ya mutu ba, an yanke shi aka ce, ƙila masu ƙwacen waya ne ki bari mu je mu gani mana" Ya fita ya kira maƙwabcinsa, ya ce ya raka shi asibiti, domin su ga a halin da Tijjani yake ciki. Ala'amin bayan ya koma gida, a falo ya tarar da jauhar, sauro yayi dandazo a kanta yana cizo, sai ajiyar zuciya take yi ta ci uban kuka. Tsayawa yayi yana kallonta, tare da jinjinawa taurin kanta. Kamar ya tsallaketa ya wuce, ya durƙusa ya kwasheta kamar tsuma ya nufi ɗakinta da ita, yana zuwa ya kwantar da ita a kan gadon, ta buɗe idonta tare da ƙura masa ido. Tsaki yayi ya fita, ta mayar da kanta ta kwantar a kan pillow. Al'amin sawun keke ne, Allah kaɗai ya san in da ya dosa, ɗazu ya gama cewa idan ba zata iya zama ba, ta tafi gida, amma yanzu ya tsinto ta a falo ya kawota ɗaki. Da safe ta dafa tea, ta kawo masa da sauran meatpie ɗin da ya so jiya, yau bai yi rejecting ba ya karɓa ya fara ci. "Master" "Mmmm" "Na iya irin wannan meatpie ɗin fa, idan ka na so ka sayo mini kayan, na iya sosai mai daɗi". Ya ce "To". Da tana jin kunyar cin abu a gabansa, amma zuwa yanzu ta saba, ta gama cin nata, ta je ta kwaso kayansa da suka bushe, tana ninkewa ta saka zare da allura, tana ɗinke masa waɗanda suka yage. Yana kallonta tana yi, shi kuma ya karkace zai kunna sigari. "Master, shan sigari yana cutar da lafiya fa, ka din ga ragewa dan Allah, kar ka yi rashin lafiya". "Kin je an yi miki allurar?" "Zan sha magani, ba na son allura ne tsoro nake ji" Tashi ya yi zaune ya ce "Ƙadangare, kwaɗo yanzu kuma allura, sannu 'yar madara. Sai ki biyani kuɗin allurar da na saya" yayi maganar yana barsawa yana gyara gefen rigarsa. Tayi dariya, jin yau ya kulata, har ya ɗan yi doguwar magana da ita. "To nawa ne, sai na tara da kaɗan-kaɗan na biya ka" yayi shiru yana cigaba da sakin hayaƙi. Ta sake gyara zamanta ta ce "Master Mp nan fa tayi kyau sosai, Allah ya ƙara maka buɗi" Ya jinjina mata kai. Tijjani kuwa ba ma ya hayyacinsa, saboda ya zubar da jini sosai da sosai saran da su Viper suka yi masa, da ƙyar aka samu ya farfaɗo. Cinyarsa sun yi masa rami da ɗan buda, likitoci sai ƙoƙarin ceto ransa yake yi. "Sai oga" "Yaya na ji shiru fa, haryanzu kuna tsare da yarona". "Na sani, trape ɗin muke setting, idan muka yi gaggawa aikinmu zai kwaɓe" "Ok ina saurarenku". Jauhar sai murna take yi, zata je registration makarantar su, dama tun da aka kawota ba ta je unguwar ba. Da safe tana ta shiri, ya fito zai fita ya ajiye mata dubu ɗaya ya ce "Ki hau mota" "Na gode sosai da sosai, Allah ya sa a fi haka, ya ƙara buɗi, ya tsare mini kai" ba shiri ya kalleta, ya ga ba shi take kallo ba, sai jujjuya dubun take yi tana murmushi. "Da ina da wata ba zan kasheta ba, ina son sabon kuɗi sosai" tayi maganar tana ƙara faɗaɗa murmushin ta. "Sai ki ɗinka ta ki saka tun da riga ce" "Kuma zata yi mini kyau fa, adawo lafiya, Allah ya tsareka" Ya amsa da "Amin" Jauhar ta ƙarasa shirinta, ta tafi makaranta, kamar yadda Baba ya ce mata ta je tayi registration, a nan ta haɗu da 'yan makarantar su, ta din ga murna sun haɗu da 'yan makarantar su, da malaman makarantar ma. Ta din ga yi wa ƙawayenta mitar ba su je gidanta ba. "Jauhar wa zai zo gidanki kina auren ɗan daba? Ba ma za a bar mu mu zo ba" Jauhar ta yi murmushi ta ce "Ku daina fakewa da haka, ni da muke tare, ya aka yi bai yi mini komai ba?" "A'a ai ke matarsa ce, mu kuwa fa" Duk da ba ta gaya masa ba, haka kawai ta ji tana son ta je gida. Ganin ko ta fita ba hanata yake yi ba, ya sanya ta nufi hanyar gida. Gaba ɗaya sun yi mamakin ganinta, Anty ta ce "Yaya, ya na ganki yanzu meyafaru?" Jauhar ta yi murmushi ta ce "Lafiya lau anty, registration na zo na ce bari na biyo, tun da kun ƙi zuwa". Kallon jauhar suke yi, su ga ko akwai wani abu na tashin hankali a tare da ita, ko alamar duka ko makamancin haka, amma ba su gani ba, sai ma wata nutsuwa ta mussaman da suka gani a tare da ita. Mama ta ce 'm"Jauhar kin kyauta, wato miji daɗi, ki ka kasa zuwa ki duba ɗan uwanki, ya kusa mutuwa" Cikin tashin hankali jauhar ta ce "Subhanallah, mama ban sani ba ba shi da lafiya ne?" "Ina fa, ya dawo daga aiki, aka samu wasu suka sassare shi". Abun ya ɗagawa jauhar hankali, ta ce musu ba ta sani ba. Al'amin yana can wurin su Walid, kansa yana yi masa ciwo, ga yana jin yanayin jikinsa kamar zazzaɓi yana son kama shi. Yana jin wayarsa na ta vibrating yayi banza. "Viper wayarka fa ta cika mini kunne, dan Allah ka ɗaga" "Ƙyale ni, kamar zazzaɓi ne zai kama ni" "To ka kashe wayar mana". "Ba zan kashe ba" "Ka duba mana ko beb ɗin ka ce take nemanka, yarinyar nan ta na kula mana da kai yasin". Viper yayi tsaki, ya sake gyara kwanciyar sa. Walid ya miƙa hannu, ya ɗauki wayar ya ɗaga ya ce "Ya aka yi?" "Ka gaya wa uban gidanka, na ga cikarsa ta shigo mana arear, duk da kashedin da na yi kar ta sake zuwa, tun da ya kwasheta. Yayi ganganci mafi girma da muni, tun tun da ya bari ta shigo, ya zo ya ɗauki gawarta a dabata!. Ayshercool 08081012143 26 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Walid ya kalli Al'amin, ya lumshe idanunsa, wasu irin jijiyoyi suka fito raɗa-raɗa a goshinsa. Yayi shiru ya ƙi ko motsawa. "Mai zamani, ba ka ji me ya ce ba ne, matarka fa yake maganar ka je ka ɗauki gawarta" "Na aiketa ne?" "Ban gane ka aiketa ba? Kai kut....." Ya ɗura masa ashar. "Idan da gaske ya kasheta fa?" Al'amin ya tashi zaune, ya ɗauki wayarsa, ya danna ya kira wata lamba. "Yeah maza" Ya ce "Ina aikin da na saku?" "Ai ta gama ta tafi ma" Ya ce "Ba tafiya a ta yi ba, gidansu ta tafi, ba ka kira ni ka gaya mini ba. Wancan garan ya ce in je in ɗauki gawarta a dabarsa, wallahi ya kashe 'yar mutane sai na kasheka kai ma" "Haba maza, cewa ka yi mu saka ido, ta shiga ta gama abun da take yi ta tafi, kuma min bi ta ba ta sani ba, ta gama ta tafi ba ka ce mu bi ta mu ga ina zata tafi ba" "Wallahi liti ka bari muka haɗu sai na saka maka ƙarfe, ka ji na rantse. Ya ajjye wayar ya yinƙura, Walid ya ce "Ina zaka je, ka ce ba ka jin daɗi, ka zauna bari ni na je" "In zauna sai ya kasheta, sannan zan je?" Yayi maganar a zafafe. Walid ya bi shi da kallo, yana son gano haƙiƙanin in da ya dosa, amma bai gane ba,  Al'amin ya sake birkicewa ya ce "Ya kasheta ko ya bar ta da rai, ba shi ne a gabana ba, tun da ba ni na gayyato ta rayuwata ba, abu mafi muni shi ne ace madaki ya kuma yi mini illa, idan haka ta kasance, kan mai uwa da wabi, zan ɗauki matakin da ya dace". Ya fita da sauri, Walid ya bi bayansa, bai ma san ina ne gidan na su ba, sai da walid ya yi masa jagora, yaran madaki suna ganin Al'amin ya shigo musu unguwa da rana tsaka, amma aka rasa mai tunkararsa, dan ba su fiye galaba a kansa ba, sai sun yi masa taron dangi. Suna tafe a hanya, liti ya kira Walid ya ce masa "Ka ce ya kwantar da hankalinsa, na yi waya tana lafiya tana cikin gidan su, zamu fito da ita lafiya in sha Allah" Walid yana gaya wa Viper, ya ce "Ka ce masa bana so" ya yi maganar yana ƙara sauri. Jauhar kuwa na can, har ta ɗora musu girki, sai zungurarta suke yi, su ji a wani hali take ciki a gidanta, da irin zaman da take yi da Al'amin, amma ta dinga waskewa, taƙi gaya musu komai. Hafsa har da tambayarta, wai wuri ɗaya suke kwana?. Jauhar ta kwashe da dariya ta ce "To zai kwana a waje ne yana da mata?". Surayya ta ce "Iyee zama da maɗaukin kanwa, wato har bakinki ma ya buɗe haka?" Jauhar ta yi dariya ta ce "Kai Anty surayya tambayata fa tayi, bari na ƙarasa na je gida ma na yi girki, kar ya dawo". A tunaninsu za su ga jauhar cikin mawuyacin hali, amma sam ba su ga alamar hakan ba. Ta shiga suka gaisa da anty lubabatu,ta din ga murna yadda ta ga jauhar, babu alamar wahala a tare da ita, ta aika 'ya'yan anty lubabatu su je gidan kakannin su, su karɓo mata shirin dutse a wurin ƙanwar anty lubabatu. Da yake duk a unguwar ne. Anty lubabtu har da harhaɗawa jauhar 'yan kayan gyaran aure na mata, ita dai ba ta ce komai ba, ta karɓa ta ce ta gode. Da ta fito daga gidan, ta lura da wasu matasa da ba ta san suwaye ba, a layin amma ba ta damu ba ta shige gida. Walida ta tare ta ta ce "Me Anty lubabatun ta baki?" Suka karɓi ledar hannunta, suka ga kayan mata da turarukan wuta da humra masu kyau da ƙamshi. Suka din ga yi mata dariya cikin izgilanci surayya ta ce  "Wai nan ba ki yadda ba ke matar aure ko jauhar? Dan Allah ya ki ke yi ke kuwa da shi, ga 'yan shaye-shaye da ƙazanta, kuma har kiss ku ke yi?" Jauhar ta yi wani irin murmushi ta ce "Yaya surayya kenan" "Gaya mana man" "To ni me zan ce? Annabi ya hana faɗa, sirrinmu ne ai" Surayya ta ce "Lallai, yau na ga illar ƙani ya rigaka aure, ni ki ke gaya wa baƙar magana jauhar? "A'a ki yi haƙuri, ba baƙar magana ba ce" Ta karɓe kayanta, ta saka a jakarta, ta cigaba da aikinta. Ta zauna tana yanka salak, sai mita take yi ba ta haɗu da yaya saifu ba, kuma baba ma baya nan" Tijjani ya fito yana ɗan tattakawa, ta din ga yi masa sannu. Tun da ya shigo layin yake ganin yaran madaki tsilla-tsilla, alla-alla yake yi ya ƙarasa ya tabattar da abun da madaki ya faɗa gaske ne ko akasin haka, idan gaske ne bai san iya adadin haukan da zai yi masa ba. Walid ya ce "Ga gidan nan" dai-dai lokacin ɗan gidan anty lubabatu ya zo zai shiga gidan su jauhar, hannunsa riƙe da ledar viva, an zubo mata dutsen shiri da kayan yi kala-kala, babar anty lubabatu ta ce a bata kyauta a matsayin jari, shi ne gudunmawarta na biki. "Kai shiga nan gidan ka ce.... Sai kuma ya yi shiru dan ya manta sunanta, sai Fatima yake iya tunawa. Walid ya ce "Ka faɗa masa sunan" Tsaki yayi ya ce "Na manta sunan, sunan wani iri ne dai haka kamar Angela" Walid ya ce "Amma kuwa ka yi asara" Al'amin ya ce "Ka ce 'yar madara ta zo in ji Master" Walid na son yin magana, ya maze ya ce "Na san ƙarya fa madaki dama yake yi bai kasheta ba". Yaron ya shiga ya fara ba ta saƙon hajiya kakarsa, na bata kyautar dutse, ta karɓa tana murna da godiya, sannan ya ce "Wani a waje ya ce wai 'yar madara ta zo" take gaban Jauhar ya faɗi. Walida ta ce "Wace wata 'yar madara, babu ita a gidan nan, in ji wa ya ce maka?" Yaron ya ce "Wai in ji Master " Jauhar ta ce "Na shiga uku, master ne, ban gaya masa zan zo nan ba, waye ya gaya masa?". Ta ce "Bari na ɗaukko jakata" Anty ta fito ta ce "wannan aikin kuma wa zai ƙarasa shi? Ai sai yayi haƙuri ta gama, kai je ka ka ce masa aiki take yi, ya dawo an jima" Buɗe baki jauhar ta yi ta ce "A'a anty kar ya gaya masa haka, kaga haidar ka ce masa... Anty ta katse ta ta ce "Fita ka je ka gaya masa haka, waye shi ba gidan sirikansa ba ne ba". Gaban Jauhar ya tsananta faɗuwa, ba ta san me hakan ka iya haifarwa ba. Mama ma fitowa ta yi ta ce "Ba zaki zauna ki cigaba da aikin ba" Viper kuwa wani marurun takaici ne ya ƙule masa a wuya, jin irin saƙon da aka aiko masa da shi, kamar shi za a aikowa da wannan banzar maganar. kawai ya sai kai zai shiga gidan, walid ya riƙe shi ya ce "Mai zamani gidan sirikanka ne fa, dan Allah kar yi wani abu mara daɗi, ka zubar mata da mutunci" "Tun da suka zaɓi su aura mini ita, sai na tabattar musu da maganata ce gaba da ta su a yanzu" kawai ya saka kai cikin gidan. Cak ta tsaya, jikinta yana tsuma, ganinsa ya shigo yana wannan takun nasa, ya ƙureta da ido, tun kafin ya ƙaraso. Tsit suka yi suna kallon ikon Allah, ya ƙaraso, ta wutsiyar ido ya kalli yaya tijjani da ke zaune a kan farar kujera, ya sauke idonsa a kan mama, su surayya sannan Anty Zakiyya ta ƙarshe. Yana ganinta ya ƙara tabattar da Rahila ce ta saka aka yi masa aure, bai ga alamar akwai mahaifiyar jauhar a cikin su ba. Ya kalli Jauhar ya ce "Ni na aiko ki zo ki ka ce mini ba zaki zo ba?" Ta ce "Dan Allah Master ka yi haƙuri" "Shut up!" Yayi maganar cikin ƙaraji, tare da ball da bokitin da aka kawo markaɗe, da kwanon salak ɗin duk suka tarwatse a wurin, ta zabura ta ƙanƙame jikinta. Ai ba ita ba, har sauran matan gidan da 'yan matan. Tijjani kuwa ɗimaucewa yayi, dan kuwa ba zai manta muryar nan ba, duk da yana tantama amma kamar muryar wanda suka yi ma aika-aika. "Dama mun yi da ke zaki zo nan? Kin zata ƙarya suke yi da suka ce za su saraki idan suka kuma ganinki a unguwar nan?" Ɗago ido ta yi cikin tsoro tana kallonsa. Ganin yadda duk ta rikice ya sanya ya saki muryarsa ya ce "Zo ki wuce mu tafi" Ta ce "Bari na ɗakko hijjabina" Mayar da idonsa yayi kan Anty Zakiyya, ko ƙiftawa ba ya yi, babu shiri ta juya da sauri ta shige ɗaki. Jauhar ta fito, da jakarta da ledojinta, ya danƙi hannunta, suka yi waje. Suna fita Surayya ta ce "Bala'i dama wannan ne mai dogon zamanin? Jaraba jauhara na cikin bala'i". Hafsa ta ce "Ni kuma abun da na gani daban, kut wallahi na ɗauka zan ga wani gardin mummuna, ji mutum hanci har baka, kai amma yayi kalar tsoro da yawa, haka yake yi mata wannan tijara" Mama ta ce "Dalla ku yi mana shiru, kalli asarar da ya yi mana, abincin ranarmu ya mayar da mu baya" mama tayi maganar a ƙule. "To mama aikin gama ai ya riga ya gama, ni wallahi na zata dukanta zai yi ma. Anty har an gudu ɗaki, bayan ita ta bayar da saƙon da aka gaya masa" Daga ɗaki ta ce "Haka kurum in tsaya ya kasheni a banza, kin ga wani huci da yake yi kamar kumurci, gashi sai kallona yake yi, ya ƙara girma fiye da yadda na san shi". Jauhar kuwa suna fita, walid ya rufa musu baya, Viper ya din ga jan ta, gashi saurinsa ya ninka nata, kamar ta hantsila, Alla-Alla yake yi su ƙarasa titi ya saka ta a abun hawa, sai dai suka yi karo da madaki da yaransa. Wata irin muguwar dariya madaki yayi, wadda ta ƙara fito da ainihin muninsa, baƙi ne wuluk kuma gabjeje, yana da jajayen idanuwa, wanda yake rambaɗa musu farin kwalli, ga wani ƙaton sara a fuskarsa a kaikaice da ya raba fuskar in to two equal parts. Sai ta ga Al'amin ɗin ta nutsatstse ne mai kyan gani, a kan madaki, ta san gidansu ta san sunansa a unguwar su, amma ba ta sanshi a fuska ba. Jikinta ya hau tsuma, Al'amin ya sakata a bayansa, ya tsaya yana fuskantar madaki, Walid ya tsaya a gefensa. "Tun da aka gaya mini matarka ta shigo unguwar nan, na ce bari in auna adadin son da ka ke yi mata. Ka san bikin ma bana nan aka yi, labari na samu ban haɗu da kai na yi maka Allah ya sanya alkhairi ba. Ƙarfin halinka ya kai, tun da ka iya ratso cikin unguwarmu ka auri 'ya. Shiyasa na so ka zama ɗaya daga yarana tun a wancan lokacin amma ka ƙi. Ya leƙa ya kalli fuskar jauhar ya ce "Ashe 'yar gidan Alhaji faruku ce, rabona da ita tun tana 'yar mitsitsiya, ashe haka ta girma ta ƙara kyau, ka bani kunya ma, wannan ai ba ta wani gama nuna ba, wannan ai ka yi mata girma, kodayeke ba a nan take ba an danne bodari ta ka, bakinta mai kyau ɗan ƙarami zai yi daɗin sha, anya wannan ba.... Wani wawan mari Al'amin ya ɗauke madaki da shi yana huci, Walid ya riƙe shi ya ce "Viper ka san me ka yi kuwa?" Al'amin ya hankaɗe shi, ya kalli madaki cikin ido ya ce "Ka daɗe da kashe Al'amin ɗin da ka raina, ka mayar abun nishaɗinka, Kar ka sake ka shiga shingena, duk wala-walar da zaka yi, kar ka ƙetare iyaka". Yaran madaki suka yinƙuro, Madaki ya ɗaga musu hannu, ya ciro wata muguwar wuƙa a jikinsa, ya ce "Bari in nu na wa duniya kai rago ne, a gaban matar taka, da ka yi dan ka burgeta" Wani irin ihu jauhar ta ƙwala, ta rirriƙe Al'amin tana kuka ta ce "Dan Allah kar ka caka masa, zaka kashe shi idan ka caka masa, dan Allah ka yi haƙuri kar ka kashe shi". Viper ya ce "Kafin ɗayanmu ya bar duniya, za a ga waye ragon, ƙazamin kare kawai" Ya sake danƙar hannun jauhar, ya keta ta tsakanin yaran madaki yayi gaba, walid kuma ya tsaya a kan hanyar yana kallonsu, dan kar wani ya bi bayansu ya illata su. Madaki ya bi bayansu da kallo, ya din ga kallon wuƙar hannunsa yana murmushi, lallai yayi sake ɗan zaki ya girma, ya fara zama barazana a gare shi. Babban abun da ya ƙular da Al'amin, bai wuce yadda jauhar take ta rusa masa uban kuka ba a cikin a daidaita sahu, bayan koma menene ita ya janyo, kamar ya cillata kan titi ya huce, yana zaman zamansa an ƙaƙaba masa ita, yanzu dole duk in da zai yi sai yana tunanin kar a cutar da ita. Bai kulata ba har suka je gida,ga wani irin ciwo da kansa yake yi, ga zazzaɓi tun a hanya ya rufe shi. Suna zuwa gida, ya wuce ɗakinsa ya bar ta. Bin bayansa ta yi, cikin marairaicewa ta ce "Dan Allah Master ka yi haƙuri, ban san haka za ta faru ba, nayi niyyar gaya maka dama idan na dawo, dan Allah ka yi haƙuri" Banza yayi mata, ya rufe idanunsa, saboda yadda sanyi yake ratsa shi, ga wani abu mai ɗaci da ya tsaya masa, ya ƙi wucewa, saboda yadda abubuwan da suka wakana a rayuwar sa, suke dawo masa cikin kansa a yanzu. Idan ya tuna abun da madaki ya faɗa a kanta, sai ya ji kamar ya kurma ihu, ya gama cutarsa, ko shi jai tsaya ya ƙare mata kallo, ya ga bakin nata ba sai shi. A marairaice ta ce "Master, Yaya Al'amin dan Allah ka yi mini magana, ka yi haƙuri ka yafe mini dan Allah, na san koma menene ni ce sila". "Get out from sight, ki tashi ki fita kafin ni na sassaraki a wurin nan" a tsorace ta tashi ta fita, tana waiwayen sa. Tana fita ya riƙe kansa, saboda yadda ya yi masa nauyi. Anty Zakiyya kuwa, Rahila ta kira a waya, bayan sun gaisa ta ce 'Ƙawata yau na ga tsiya da wasali" "Bani na sha meyafaru?" "Yau ɗanki ya zo gidan nan ai" "Wa kenan" "Sirikinmu mana, wai ashe yaran madaki ɗan dabar nan na unguwarmu sun ce idan ta sake zuwa unguwar nan, sai sun sassarata, ta zo gidan nan bai sani ba, a sukwane ya taho, yau mun ga bala'i, kin ga tijarar da ya yi ya ja hannunta suka tafi?" Rahila ta ce "Zai aikata fiye da haka ma, in dai Aminu ne ɗan banzan bawa kenan ake gaya miki" "Taɓ amma anya ba son yarinyar nan yake yi ba? Kin ga a yadda ya zo kuwa?". "To ke ina ruwanki, dama dai ba burinki ita wannan ta bar miki gida ba, shi ya sani ba mace ba ce ba? Luf zai yi ai, ni fa tun da aka yi auren ba mu sa shi a idonmu ba, na ce can ya ƙarata" Suka kwashe da dariya, Zakiyya ta ce "Taɓ amma ƙato ne, sai ka ce ɗan dambe, kuma wallahi ba wani abun gyara da muka yi mata, yau ne ma da ta zo maƙwabciyarmu ta bata, amma haka nan muka kaita" "Oho musu, in dai buƙata ta biya, ba shikenan ba, su ƙarata" Suka kwashe da dariya gaba ɗaya. Jauhar ta kasa zaune ta kasa tsaye, master ya ɗau fushi da ita, gashi ya ƙi fitowa, kuma ya korota daga ɗakinsa. Da canjin hannunta, ta haɗa ta sayo fulawa, ta kwaɓa alkubus, da wata irin miya ya 'yan dabaru, sai dai har ta yi ta gama bai fito ba. Sai ta kasa ci, ta sake lallaɓawa ta leƙa ɗakinsa, ta ga yana banɗaki, ta cigaba da tsayuwa ya fito, ta tsaya tana sallama a bakin ƙofa. "Idan ki ka bari na zo na sameki a wurin nan, sai na ɓata miki rai" Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri master, na tuba ba zan sake ba" Kwanciya ya sake yi, ya juyawa ƙofar baya. "To in kawo maka abinci?" Kamar ya ce eh, amma yayi mata shiru. Abun da ya ɗaure mata kai, bai wuce har dare kwanciya yake yi ba, yaƙi fitowa, cikin tsananin fargaba ta shiga da kwanukan abinci ta ajiye masa. Ƙamshin miyar da ya cika masa hanci, ya sanya ya buɗe idonsa. Gwiwoyinta ta saka a ƙasa ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri, ni ko wani hukuncin ka yi mini dan Allah ka daina yin fushi da ni, bana son na ga na yi laifi dan Allah" hawayenta ne yake ɗiga a kan katifarsa, ya gyara kwanciyar sa ya juya mata baya. Ya tsani kuka, ba ta san ƙara ƙular da shi take yi ba. Tashi ta yi ta sake zagayawa kamar mayya, tana yi masa magiya. Ya buɗe jajayen idanunsa yana kallonta, sai dai yaƙi magana. Yarrrr haka ta ji tsigar jikinta tana tashi, ba ta san kallon ma yake yi mata ba. "Ka yi magana Please, ka ce ka haƙura" tayi maganar tana jan majina. Ƙafarsa ya ɗora ɗaya kan ɗaya yana kaɗawa, saboda ciwon da kansa yake yi, amma a zahiri abun da yake yin, kamar yana yi ne da gayya da nuna mata iko da izza irin ta ɗa namiji. "Kin cika mini kunne" yayi maganar a hankali, duk da buɗɗaɗiyar murya ce da shi irin ta jaruman maza. "To ka ce ka haƙura mana" tayi maganar cikin shagwaɓar da ba ta san ta yi ba. "Kai mini ruwa zan yi wanka" cikin sauri ta ce "To" Tunani yake yi daban-daban a ransa, ya ma rasa wanne zai yi, yana shiga wankan, ta sake gyara shimfiɗar katifarsa, ya yi wanka ya fito yanzu ma jikinsa babu riga, yana ƙoƙarin mayar da kayan da ya cire, da sauri ta ce "Ai kana da wankakkun kaya, na wanke maka ka saka wannan" ta yi maganar tana miƙo masa kayan da ta ciro masa. "Ɓace zan canza kaya" ta fita da sauri,mintuna goma da ta dawo, tuni ya kusa rabin abincinsa. Garin ta miƙa hannu ta ɗauki jug ta zuba masa ruwa, hannunta ya taɓa ƙafarsa ta ji zafi sosai, ta kalleshi ta sake kai hannunta ƙafarsa. "Master zazzaɓi ka ke yi?" Lomarsa ya cigaba da yi, cikin tsoro ta sake kai bayan hannunta ta taɓa hannunsa. "Na shiga uku ba ka da lafiya ai, duk ni na janyo ko?" Ya karɓi jug ɗin hannunta, ya cire murfin, ya kafa kai ya sha fiye da rabin ruwan, sai ka ce tsohon raƙumi. Ya gama ya jingina da jikin bango ya sake lumshe ido. "Master, akwai allurar nan da ka sayo mini ba ayi mini ba, mu je in raka ka ayi maka to" Gyatsa ya saki, maimakon ya yi hamdala, sai ita ta ce "Alhamdilillahilazi aɗa'amana haza, Ubangiji Allah ya ciyar da mu kullum, ya bawa wanda bai samu ba" "Amin" ya faɗa ƙasa-ƙasa zai kwanta, a sukwane ta ce "Dan Allah kar ka kwanta, mu je a duba ka, kar ka sha wahala, sauro ne yayi yawa a unguwar nan shiyasa muke ta zazzaɓi, dan Allah ka zo mu je a duba ka" "Kai wallahi kina addaba mini, kin dame ni" Jauhar ta kwantar da murya cikin sigar rarrashi ta ce "To na sani, amma ka yi haƙuri, na daina, dan Allah mu je a dubaka ka ji Mijin 'yar madara, ba ka ji yadda jikinka yayi zafi ba?" Ya kalli yadda ta dafe kafaɗarsa, tayi saurin sakinsa, ya ce "Sai an yi sallar magariba" "To mu koma falo, sai na saka maka maganin sauro a ɗakin, idan ka cigaba da kwanciyar jikinka mutuwa zai yi" Da ƙyar ta lallaɓo shi, suka dawo falo, ta kunna maganin sauro. Ana idar da sallar magariba, ta ɗaukko allurar, ta ce su tafi, ya ce ya fasa zuwa, shi ba zai iya tafiya ba. Da ƙyar sai ka ce ɗan goye, ta lallaɓa shi suka fita. Ta rufe ƙofar gidan, ta riƙe hannunsa ta ce "To mu je, kar ka ji jiri idan ka gaji ka yi mini magana sai mu tsaya ka huta". Kallonta kawai yake yi, ɗan hannun nata ɗan mitsitsi a cikin nasa. Suna tafe tana ƙara ba shi haƙuri, a kan laifin da ta yi. Nasiru mai chemist na ganinsu ya ce "A'a jauhar, kin warware shi ne shi ma ya kwanta" tayi murmushi ta ce "Allura na kawo shi, ayi masa mai sanyi dan Allah" Da jauhar ta san yadda yake ji a zuciyarsa idan ya ga tana tankawa mai chemist da ba ta yi ba, sai dai bai san dalilin hakan ba, kawai ba ya son ya ga wani yana kulata. Aka gama yi masa suka fito za su tafi, ta tsaya tambayar mai ɗanyen dankali nawa kwano. Al'amin ya zaro kuɗin ya bayar, suna tafe tana godiyar dankali. Da safe ta soya musu dankali da tea, ya gama karyawa, ya kalleta ya ce "Wannan matar da na gani a gidanku wacece?" Ta ce "Wacce?" "Mai baƙaƙen kayan nan" "Anty zakiyya ce, matar Baba ce" ya jinjina kai bai sake cewa komai ba. "Ka santa ne?" Yayi shiru bai amsa ba, daga haka ta ja bakinta tayi shiru. Babu yadda ba ta yi ba, a kan ya je a ƙarasa allurar nan, amma ya ƙi. Da ya ji ƙwarin jikinsa ma, fita ya cigaba da yi. Jauhar na zaune a falonta, tana tunanin ƙirƙirar sabbin styles na abun hannu da jigida, ta fara sayarwa. Aka bubbuga mata gate, ta tashi ta je ta buɗe, ta ga wani mutum da ba ta san shi ba, fuskarsa sanye da facemask ya ce "Mai zamani yana nan?" Ta girgiza kai ta ce "Ya fita" "Ga wannan ki ajiye masa". Ya bata leda mai baƙi da fari. Ta karɓa ta ce "In ji wa zan ce?". "Idan ya zo zai gane, ki ajiye masa a ɗakinsa, zan kira shi" Ta ce "To shikenan" Ta rufe ƙofa, kamar ta buɗe, sai ta fasa ta kai masa cikin drower sa, ta ajiye masa ta cigaba da sabgoginta. Kayan da anty lubabatu ta bata ta ɗauka tana duddubawa, ta ɗan ɗanɗana abun, tayi shiru tana tunani, ita sam abun da ake faɗa a auren, ba ta ga alamar sa ba, dan shi ba ta tata ma yake yi ba, ya ƙule a ɗakinsa yayi shaye-shayensa ya ci abinci ya fita yawonsa shi ne kawai a gabansa. Ta ɗan taɓe baki, ta ɗauki turaren wutar, ta tirara na gidan, ta turara na jikinta, ta ɗora girki. Da daddare da wuri ya dawo gida, gidan sai ƙamshi yake yi na musamman, giftawar farko da tayi, sai da ya ɗaga kai ya kalleta, ƙamshin har cikin ƙwaƙwalwarsa ya ji shi. Yau  faten dankalin ta yi, dan shi ne kawai da su, sai dai yayi masa daɗi bai taɓa sanin ana faten dankalin hausa ba, sai yau da ta bashi, har mamakin yadda take sarrafa abinci yake yi. Ya gama cin abincin ta ce "Master yanzu allurar nan dai ba za a ƙarasa ba ko?" "Eh" ya faɗa kai tsaye. "Ai shikenan, thank God tun da ka warke ai. Ka yi mini addu'a mun kusa fara WAEC, Allah ya sa result ɗina yayi kyau". "Sai ki yi karatu" "Ina yi ai" ya kalleta ya ce "A hakan, kina shirme dai" ta gane da kayan beat ɗin ta da stone yake, tayi murmushi jin yadda yau yake yi mata doguwar magana. "Ina karatu sosai da sosai fa". "Akwai kwaɗo a ƙarƙashin kujerar nan da ki ke" da sauri ta kalli kujerar, sai kuma ta yi dariya ta ce "Ai na daina jin tsoron" wai nan tsokanarta yake yi, amma fuskar nan a haɗe. Har wajen ƙarfe goma suna tare, yana ta danna wayarsa, mai madannai, ita kuma tana jin radio tana aikinta, ba hira suke yi ba, amma kasancewar su a hakan ma, daɗi take yi mata. Ya yi miƙa ya tashi zai tafi ɗaki ta ce "Tafiya babu sallama" Ba tare da ya yi Magana ba, ya ɗaga mata hannu, murmushi ta yi ta ce "Asuba ta gari mijin Angela" ɗan rausayar da kai ya yi kamar zai yi murmushi ya shiga ɗakinsa. Ya kwanta yana shaƙar ƙamshin da bedsheet ɗin sa yake yi, bai taɓa tunanin zai yi aure ba, dan babu wannan lissafin a gabansa, ba dan albarkacin auren ba, da a cikin tsummokara zai kwana a can gidan da suke tare da su Walid. Tsakar dare jauhar ta ji motsi, kamar ana watsi da kaya. "Malam kar ka shiga wannan ɗakin ba komai a ciki, mata ta ce a ciki, kuma babu in da shari'a ta baka damar shiga in da matata take" Jin muryar Al'amin, ya sanya ta saukko daga kan gadon da sauri, wata irin dalleliyar fitila aka saka ana haske gidan. "Shut up, kar ka sake magana, kar na sake jin bakinka" Cikin ƙaraji ya ce "Sai na yi magana, wallahi ka shiga ɗakin nan, zan illataka". Da gudu ta fito dan ta ga meyake faruwa, ma'aikata ta gani, har da jami'an tsaro, sun saka wa Al'amin ankwa sun durƙusar da shi a kan gwiwoyinsa. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Yallaɓai me yayi muku? Laifin me ya yi?" "Ki koma ɗaki Ki nemi hijjabi ki saka" yayi maganar cike da takaici. "Oya ku yi searching ko ina a gidan nan, kar ki motsa daga in da ki ke" Wani jami'in ne ya fito daga ɗakin Al'amin, da wannan ledar da aka kawo aka ce a ajiye masa, ya ce 'Ga abun da muka samu sir" Shugaban operation ɗin ya karɓa, ya zazzage sai ga ƙwayoyi, da allurai da wiwi da sauran tarkace sai kuma wata 'yar leda mai ɗauke da wani farin gari. Ya ce "Good, mu tafi da shi mun samu abar" "Yallaɓai, wallahi wani ne ya kawo su ɗazu, ba shi ya kawo su ba, dan Allah kar ku tafi da shi.  Ko kallonta ba su yi ba, suka tasa ƙeyar Al'amin. Ayshercool 08081012143 27 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Biyo bayansu tayi, tana wani irin kuka mai ban tausayi, tana yi musu magiyar su sake shi, ba shi da laifi, amma babu wanda ya saurareta a cikinsu. Maƙwabta na jiyo kukanta, amma babu wanda ya iya ko leƙowa ya ga abun da yake faruwa. Shi kuwa Al'amin ko a jikinsa, kukan da take yi ne kawai ba ya so. Suka saka shi a mota, ta ce "To Yallaɓai ina za ku kai shi dan Allah" "NDLEA, daga nan zamu miƙawa 'yan sanda shi, su kai shi gaban kotu". "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yanzu dai sai kun kai shi NDLEA ɗin kenan? Wancan karon baku kai shi ba sai yanzu, dan Allah ku duba lamarin nan" Suka saka Al'amin a mota, suka tafi da shi, a falonta ta zauna, ta fashe da kuka, ta daɗe a wurin tana kuka, ganin hakan ba mafita bane, ya sanya ta tashi ta ɗauro alwala ta koma ɗakinta, tayi ta sallar da ba ta da tabbacin tana karanta ayoyin daidai saboda tashin hankali, ta ɗaga hannu tayi addu'a, amma ta kasa kawai ta mayar da kanta sujuda ta fashe da kuka. Har asuba ta yi idonta biyu, ta yi sallar asuba ta idar, ta zauna tana karanta duk abun da ya zo bakinta, wani abu mai nauyi ya tokare mata ƙirji, ta ji tamkar numfashinta zai ɗauke gaba ɗaya. Bayan sallar asuba magidantan layin suka tsaya suna salallamin, jiya da daddare ma'aikatan sun shigo layin, amma babu wanda ya fito. Malam lawan ya ce "Har kwa tambayi lafiya? Ai tun da ɗan daba ya tare muku a unguwa, sai abun da Allah ya yi, wurinsa suka zo, wataƙila ma wata ta'asar ya je ya tafka, suka zo suka yi masa ɗaukar amarya tsakar dare". Suka yi ta salallami da fatan Allah ya kyauta. Har rana ta yi haske, jauhar tana zaune a wuri ɗaya, idanun ta sun yi ja, duk sun kumbura fuskarta tayi ja ta kumbura saboda kuka. Maman halimatu da wata mata mai kallon gidan na jauhar suka shigo, sai da suka yi ta sallama, da ƙyar ta iya amsawa sam ba ta ji sallamar ta su ba ma, ta fito falo ta ce su shigo. Maman halimatu ta ce "Jauhar, lafiya kuwa? Wai meyafaru ne jiya mun ji hayaniya, babu damar mu fito. Take wasu hawayen suka ziraro mata ta goge su ta ce "Jami'an tsaro ne suka  zo suka tafi da shi" "Subhanallah, laifin me yayi?" Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba" "To ki yi haƙuri, ki samu ki ci abinci,  sai ki nutsu a san abun yi, Allah ya kyauta ya kiyaye gaba" Ta amsa musu da to ta gode. Kai ka ce takaba take yi, duk ta fita hayyacinta, ba ta san wurin wa za ta nufa da maganar nan ba, kuma ba ta san ina hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyin take ba ma, balle ta je, ba kuma ta san ta tambaya a gano wani abun, gashi ko gidan su Al'amin ɗin ma ba ta sani ba, balle ta je ta gaya musu, ko da wani abu da za ayi a kai. Ta dudduba ta tattara ɗan kuɗin da take da shi, ta fita, ta samu mai napep ta tambaye shi idan ya san ina ne hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi. Ya ce mata ya sani, ya ɗauke ta ya tafi da ita. Ta din ga yawo a cikin hukumar, aka ce mata ba ya wurin, ba a kai shi ba, sai da ƙyar aka ce mata yana nan, amma ba zata ganshi ba, babu irin magiyar da ba ta yi ba, amma suka hanata ganinsa, ƙarshe sai gida ta koma a matuƙar galabaice. Ta rama salollin da suke kanta, ta din ga addu'a da fatan Ubangiji Allah ya fitar da shi lafiya, da ta san abun da zai faru kenan, da ba ta karɓi abun da ba ta san ko menene ba ta ajiye masa. Ɗaya maƙwabciyar ta ta wasila, wadda mijinta ya taɓa raka su wurin mai chemist ta shigo gidan. Ta ce "Jauhar yaya ake ciki, kin same shi kuwa, kin je wurin 'yan sandan?" Ta ce "Eh na je, ba su bari na ganshi ba" "Kuma ba su gaya miki abun da yayi suka kama shi ba?" Ta jinjina mata kai alamar eh, wasu hawaye masu ciwo suna zubo mata. "Ki yi haƙuri ki kwantar da hankalinki jauhar, in sha Allah komai zai wuce kamar ba ayi ba, kuma in sha Allah zai fito" Ta ce "To Allah ya sa". Yau ma haka ta kwana salloli, da kai wa Allah kukanta, da fatan Allah ya saka mijinta yana lafiya ya kuɓutar da shi. Da safe ta sai ƙosai da buredi, ta dafa tea, ta kuma wanke ƙafa ta koma wurin nan, amma suka sake ce mata ba za ta ganshi ba, tayi magiyar har ta gaji, ta basu abincin ta ce su bashi. Ta koma harabar wurin, ta nemi wuri ta zauna, ta rasa abun da yake yi mata daɗi, rabonta da abinci tun a jiya, gaba ɗaya tunanin halin da Al'amin yake ciki, da wanda zai shiga a nan gaba ya dame ta, ta gaji da zama ta tashi ta nufi gida. Ɗakinsa da suka shiga duk suka watsar da kaya ta shiga, dan damuwa ba ta bari ta shiga ta gyara ba. Duk sun watsar da komai na ɗakin, ta tattare masa kayan, tana cikin gyarawa ta gano wayarsa, ta ɗauka tana duddubawa sai ta ga tarin kiran walid da liti, cikin hanzari ta kira lambar walid. "Ya ne maza? Tun shekaranjiya ban sake jin ɗuriyarka ba, na zo gidanka ba kowa ka kuma ƙi ɗaga waya". "Assalamu alaikum" tayi masa sallama. Ya ce "Ahh madam ke ce ashe? Ya ake ciki yana ina?" Muryarta na rawa ta ce "Shekaranjiya da daddare jami'an tsaro sun zo sun tafi da shi" "Kamar yaya? Me yayi?". "Abu aka kawo aka ce na ajiye masa, su kuma suka zo da daddare suka ga kayan a leda, suka tafi da shi na je sun hanani ganinsa" tayi maganar cikin kuka. Walid ya ce "Ya isa haka yi shiru, bari na zo gidan gani nan" Sai ta ɗan ji sanyi a ranta, tamkar yana zuwa zai fito mata da Al'amin ɗin. Kusan awa ɗaya da rabi, ta ji ana knocking gate. Da sauri ta tashi ta je ta buɗe, liti ta gani da Walid, har ƙasa ta durƙusa ta gaishe su. Walid ya amsa ya ce "Ya aka yi, meyafaru?" "Yadda dai na gaya maka, wani ne ya kawo wata leda ya ce a ajiye masa, na manta ban nuna masa ba, kawai suka zo cikin dare suka tafi da shi, naje na je hukumar sun hana ni ganinsa" Liti ya ce "Ki yi haƙuri, ki daina kukan haka, kuma kin tabattar bai yi wani laifin ba?" "Ni dai a iya sanina bana tunanin yayi wani abun, duk da ba tare muke yawo da shi ba, amma dai sun ce a kan kayan da suka gani a gidan nan ne" Walid ya ce "Ki kwantar da hankalinki, in dai Viper ne, mutum ne mai sa'a koma menene zai fito, amma ki kwantar da hankalinki, yanzu idan muka je babu lallai su sauraremu, amma in sha Allah gobe in Allah ya kaimu da wuri zamu je mu ga yadda za ayi". Ta ce "To shikenan na gode sosai, bari na kawo muku ruwa" "Kar ki damu a ƙoshe muke, ki kwantar da hankalinki idan da wani abu ki kira lambata" Ta ce "To na gode" Ta rufe ƙofa suka tafi, liti ya ce "Ikon Allah" "Menene?" "Kawai rayuwar Mai zamani nake kalla, yadda yake gararambarsa da kamar babu mai so, idan muka faɗa cakwakiyarmu, iya mu muke warware kayarmu, babu wanda ya damu da mu, shi kalli Allah ya kawo masa mai kula da shi". "Haka ne, amma tausayi ta bani wallahi, yarinya ce sosai. Yana ta buyagi da rashin mutunci an yi masa aure, amma sai da ya mari madaki saboda ya tankata". Liti ya kwashe da dariya ya ce "Kai mace fa aka ce maka, na raba ka" Walid ya kwashe da dariya ya ce "A ƙi faɗinsa, da madaki ya ce ya kashe ta, mazewa yayi ba zai motsa ba, wai ba shi ya aiketa ba, amma ka ga wasu jijiyoyi da suka tashi a goshinsa, ga wani gumi da yake a iya karan hancinsa, bai san yana wasu abubuwan ba" suka sake kwashewa da dariya. Liti ya saka su guduma ɗan gidan mai unguwa, su din ga kaiwa sun komowa, suna ɗan zagaywa a layin gidan viper, idan suka ga wani abu da ba su yadda da shi ba, su sanar masa. Suka cigaba da kaiwa suna komowa a hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi, amma su ma ba su samu ganin Viper ba, suka ce sai dai idan sun kai shi wurin jami'an tsaro su je can su ganshi. Hankalin Jauhar ya ƙara mummunan tashi, ta rasa in da za ta saka ranta ta ji daɗi. Ta sake amfani da wayarta, ta kira walid a waya, da yake sun ce kar ta sake zuwa hukumar, ta bari za su din ga zuwa su. Ta duba wayar kaf, babu sunan wani mutumin kirki a ciki, balle tayi tunanin akwai lambar wani ɗan gidansu,  ta kira duk sai sunayen su Liti da ire-iren su. Sai kuma ta fara tunanin ko ba shi da kowa ne? Amma da ba shi da kowa ai ba zata ga kakarsa ba, kuma an nuna mata Rahila ranar da aka yi bikinsu Anty Zakiyya ta ce mata wai babarsa ce, amma tana tantama tun da aka yi auren, bai taɓa kai ta gidansu ba, kuma babu wani wanda ya zo daga gidan. Walid suka Kuma dawowa suna rarrashin ta, a kan suna ta ƙoƙarin ganin ya fito, ta gaza haƙuri ta ce "Dan Allah to ina ne gidansu, yakamata ace sun sani" Walid ya ce "Taɓ ke 'yan gidan na su da suna ta tashi, da baki gansu ba, ki manta da maganar su kawai ki cigaba da addu'a". Ta ce "Amma kamar yakamata a gaya musu halin da yake ciki, ko ba za su yi komai a kai ba". Walid zai yi magana, liti ya ce "Bari na kwatanta miki gidan na su" yayi mata kwatance sannan suka yi mata sallama suka tafi. Liti ya ce "A irin wannan yanayin da take ciki, idan ba ka kwatanta ba sai ta tsaneka ai, idan ta je ta ganewa idonta shikenan" "Haka ne, amma ka san wannan matsiyaciyar matar gidan na su ba mutunci gareta ba, kar ta ƙara mata zafi". Suka cigaba da tattaunawa. Kusan kwanaki bakwai da kama Al'amin, idan ka ga jauhar sai ka ce tayi jinyar shekaru, duk ta ƙare ta fita hayyacinta. 'yan sana'oin ma ba ta iyawa, saboda tunani da damuwa. Liti ya zo da safe, tana falo tana karatun Alkur'ani, ta ga kiran waya a wayar Viper, ta tashi ta fita ya ce "Sako hijjabinki mu je, sun bawa 'yan sanda shi, idan Allah ya taimake mu, wataƙila mu ganshi" cikin tsananin zumuɗi, ta yafo mayafinta, ta rufe gidan suka tafi. Sai dai da suka je ɗin ma, tsugono ba ta ƙare ba, dan sun fi ƙarfin awa biyu, walid da liti suna safa da marwa, da faɗi tashin su ga Al'amin, Jauhar addu'a kawai take yi, tun da ta ga haka ta san lamarin ba ƙarami ba ne. Da ƙyar aka ce za su ganshi, aka tafi da wasu wani wuri, suka jira a reception ɗin sashen. Babu tsammani ta ɗaga kai ta ga yana tahowa, yana ɗingisa ƙafa, cikin hanzari ta miƙe tsaye ta zuba masa ido, kansa a ƙasa jami'an tsaro sun taso shi a gaba, su liti ma miƙewa suka yi tsaye, da ya kusantota sai ta ga jikinsa duk alamar duka, gefen fuskarsa a kumbure, haka wuyansa, shirt ɗin jikinsa tayi datti, duk busasshshen jini, take jikinta ya hau tsuma cikin tashin hankali. Ya zo ya nemi wuri ya zauna kamar basarake, gabansa ta ƙarasa cikin tashin hankali muryarta na rawa ta ce "Master, dukanka suke yi haka?" "Maza wai meyafaru ne? Me ka yi haka aka kawo ka nan?" Walid ya tambaye shi cikin damuwa. Jauhar ta ce 'Yallaɓai, dan Allah ku sake shi, dan Allah ku yi haƙuri ba zai ƙara ba, wallahi kayan da ku ka gani a gidan lafina ne, bai san da su ba, dan Allah ku yi haƙuri ku sake shi" Ɗaya daga cikin 'yan sandan ya kalleta ya ce "Yarinya yayanki ba ya ji, ba zamu sake shi ba, wanda aka kama da cocaine ki ke cewa a saki ba shi da laifi? For more than 7days ya amsa laifinsa yaƙi, ga kaya an kama shi da shi, yayi magana yaƙi kamar dutse" Gaba ɗaya sak suka yi suna kallon ɗan sandan. "Wace irin cocaine kuma? Ka ga malam ba ma son rainin wayo, haba kai tare fa muke sabgar nan da shi, a gidan uwar wa zamu ga cocaine ɗin?" Walid ya yi maganar a matuƙar fusace. Cikin tsawa wani ya ce "Kai ka san a ina ka ke?" "Na sani mana, ai ba lahira ba ce, balle ace mutum ta sa ta ƙare, ƙarshen abun dai ku kashe mutum, kai da muna harka da cocaine zaku ganmu a haka ne?" Jauhar ta yadda sai hali ya zo ɗaya ake abota, daga Al'amin har abokansa ba su da tsoro. Fashewa ta yi da kuka ta ce "Wallahi Yallaɓai zan iya rantsewa ba ya ta'amalli da cocaine, bai san ma in da zai same ta ba". "Yayi bayani da bakinsa mana" Cikin hanzari ta koma wurinsa, ta ce "Dan Allah Master ka yi musu magana ko zasu ƙyale ka mu tafi, ka gaya musu ba taka ba ce ba, laifina ne" Yadda ginin wurin ba ya motsi, balle yayi magana haka Al'amin yayi kirim a wurin. "Dalla malam ka yi musu bayani, ka gaya musu ba ka ta'amalli da ita kar su yi ta tila maka na jaki a banza su nakasa ka" Walid yayi maganar cikin ƙunar rai, dan ya san ƙage kawai aka yi wa Al'amin. Liti ya ce "Kai ma ka san ba zai yi ba, wasu lokutan zuciya in dai irin ta shi ce ba ta yi ba" Jauhar ta riƙe hannunsa za ta yi magana, sai dai jikinsa kamar wuta Saboda zafi, sai yanzu ta tuna bai gama warkewa ba aka kama shi, durƙushewa tayi a gabansa ta cigaba da kuka. "Lokacinku yayi, zaku iya tafiya" Liti ya ce "Ko ba ku ce ba zamu tafi, kowa yayi na gari dai kansa ya yi wa" Al'amin ya miƙe tsaye, ya saka hannu ɗaya ya ɗagata daga durƙushen da take, ya juya zai koma, ta saka ƙarfinta ta rirriƙe shi tana kuka. "Ke wai meye haka, da ki ka samu aka bari ki ka ganshi" ɗan sandan ya daka mata tsawa. "Wallahi sai dai ku rufe mu tare, ni ba zan tafi ba, wai ya ake so na yi ne? Ya zan yi ko ina babu daɗi, ni komai nawa ba sa'a. Na gaya muku ba shi da laifi, amma dukansa ku ke yi, tayaya hankalina zai kwanta idan na tafi? Ba laifinsa ba ne wallahi, laifina ne na karɓi abu daga hannun wanda ban sani ba dan Allah ku ƙyale shi" Matsanancin tausayin da jauhar ta bawa liti, ya sanya ya fice ya bar wurin, kuka take iya ƙarfinta, Al'amin har mamaki yake yi, tsakaninsa da ita ba wata shaƙuwa ko kulawa ta musamman amma idan abu ya same shi, gaba ɗaya sai ta rikice. Walid tsayawa yayi ya ga viper zai rarrasheta ko kuma ƙasaitar zai tsaya ya cigaba, da kuwa ko 'yan sandan za su rufe shi, sai ya zage shi. Ɗaya daga jami'an tsaron yayo kan jauhar, da nufin ya ɓanɓareta ta ƙarfin tsiya, su mayar da Viper, cikin hanzari ya ja baya da ita a jikinsa, ya ɗaga masa hannu yana ƙara tsuke fuska. Ya saka hannu, ya ɓanɓareta daga jikinsa, ya riƙe hannayenta, gaba ɗaya kammnin fuskarta sun canza saboda idanunta sun kumbura sosai ta koma pink saboda kuka. Ya sunkuyo dai-dai fuskarta ya ce "Kin kusa fara exam, ki yi karatu sosai, kar ki zauna zaman shiriritar nan, ki yi ƙoƙari ki yi karatu ki zama lawyer ko likita, ko dan saboda fitinannen mijinki, ki gaida mini da kwaɗinki da ƙadangaru idan kin koma gida" tana jin yadda jikinsa yake fitar da hucin zafi da warin datti, kwana bakwan nan babu alamar wanka ko wadataccen abinci a tare da shi. Ya kama kafaɗarta, ya saita ta hanyar fita ya ce "Kar ki sake zuwa wurin nan saboda ni" ya kalli walid ya nuna masa Jauhar, ya yi masa wata inkiya, ya juya suka mayar da shi. Suka fito tana kuka, liti ya girgiza kai ya ce "Wallahi Mutanen nan 'yan wuta ne" Walid ya ce "Kai wannan hurumin Ubangiji ne, amma ko dan hakkin yarinyar nan Allah sai ya kama su, a gidan uwasu zai ga cocaine ɗin, wallahi ƙila su suka zo da abar su suka saka masa" "Zasu aikata ai ba tsoron Allah suke yi ba" sun yi gaba suna ta surutu suna zage-zage da tsine-tsine. Suka nemi jauhar suka rasa, suka waiwaya, tana bakin ƙofar in da suka baro, ta zauna dirshan tana matsar hawaye. Liti ya ce "Taɓ lallai sabga da mata sai haƙuri, wannan ko mutuwa yayi abun da za ta yi kenan" Walid ya ce "Sai an yi mata uzuri, ba ta saba ganin wannan tashin hankalin ba, ina zuwa". Ya koma da baya wurinta, ya zauna ya din ga rarrashinta, tare da ba ta tabbacin Aminu zai fita. Cikin kuka ta ce "Ba ma fa shi da lafiya, zazzaɓi ne a jikinsa" "Ki yi haƙuri, Allah zai bashi lafiya" Ta sake cewa "To yanzu daga nan me za su yi masa?" "Wallahi ba mu sani ba, amma zamu cigaba da bibiya in sha Allah, sai mun ga abun da ya ture wa buzu naɗi" da ƙyar ta taso, suka kaita har gida, Walid ya ba ta kuɗi, ta ce ba zata karɓa ba, sai da ya ce mata Al'amin ne ya ce ya bata sannan ta karɓa. Har ta shiga falo, aka buga mata ƙofa, ta dawo ta buɗe, ta ga Malam lawan baban su halimatu a tsaye. Ta durƙusa ta gaishe shi, ya ce "Wato duk na san ke da mijinki, kuna jin haushina, amma ni duk in da gaskiya take sai na faɗa. Ke yanzu ki ji da halin da mijinki yake ciki, amma kin zo kina tara mana maza a layi, kusan kullum sai sun zo, shi fa aure abu ne mai daraja da muhimmanci". Jiki a sanyaye ta ce "Tara maza kuma?" "Eh mana, wannan da ku ke fita tare da su ku dawo, muharraminki ne?" Kalmar ta yi mata nauyi sosai, amma ta dake ta ce "Aboknsa ne, su ne suke taimaka mini a kan case ɗin sa" "To ke me yayi miko zafi? Ki koma gidanku mana, idan ya fito kya dawo, ko ma ki haƙura da auren, da kyanki da ƙuruciyarki nan da nan wani zai aureki, shi kuma ya cigaba da shashancinsa". Ta ce "To na gode sosai" "Ai gara dai ki san abun yi, ni Allah ya sa ma ba iyayenki ki ka bujirewa a kansa ba, Allah yake jarabatarki ba" gaba ɗaya sai ta ji kimarsa ta zube a idonta. Jauhar ta kama Alƙur'ani da da carbi, tayi ta Addu'a tana gaya wa Allah. Aka sake shafe kwana biyar, su liti suna yi mata yawo da hankali, suka kuma hanata komawa wurinsa, sai su ce mata sun je yana lafiya yana gaisheta. Haka kurum ta ji a ranta ƙarya suke yi mata, ba tare da sun sani ba, ta sake ɗaukar ƙafa ta tafi wurin 'yan sanda, har da abincinta ta tafi da shi, sai dai suka tabbatar mata sun kai shi kotu, har alƙali ya aike da shi gidan gyaran hali, zuwa lokacin da za a cigaba da shari'a. Cikin tashin hankali ta tambaye su, zuwa yaushe zai fito. Suka ce mata ta tafi kotun ta tambaya, suka din ga yi mata wasa da hankali, har da wanda suka biyota da maganar lalata. A ƙofar gida, ta tarar da su walid, sai jan ƙafa take da ƙyar, ta ƙarasa. Walid ya ce "Madam ina ki ka tafi ne, mun zo ba kya nan?" Ta kalleshi cike da karaya ta ce "Dama an kai shi prison ba ku gaya mini ba?" Liti ya ce "Komawa ki ka yi kenan, ke ana ta ɓoye miki, dan kar ki tayar da hankalinki, shi muka zo gaya miki, sai da muka tsara yadda zamu gaya miki, yadda ba zaki damu ba, amma kin tashi kin tafi kin jiyo wa kanki damuwa" Ta ce "To ya zan yi, na kasa jurewa". Walid ya ce "Yanzu dai tun da kin riga kin je kin ji da kanki, shikenan amma ki yi haƙuri zamu nemo wata hanyar mijinki zai fito in sha Allah" Jinjina musu kai kawai tayi, ta shiga gida. tuna da liti yayi mata kwatancen gidan su Al'amin, kamar korarriya, ta sake ɗaukar hanya, ta tafi unguwar su Al'amin tare da fatan Allah ya sa idan ta je gidan su Allah ya sa a dace a samu hanyar fitar da shi. Sai da ta haɗa da tambaya, sai dai gidan na su ba ɓoyayye bane ba, mussaman ma sunansa da ya riga ya shahara sosai. Sau biyu tana sallama aka amsa, mata wata matashiyar budurwa, da zata girme mata ta leƙo ta amsa. Ta ce "Ya aka yi?" Jauhar ta yi murmushi ta ce "Baƙuwa ce" Amira ta ce "Baƙuwa daga ina?" Rahila ta ce "Amira ki bari ta shigo mana" Ta bawa jauhar hanya, ta ƙarasa ta shiga falon da sallama. Rahila na ganinta ta washe baki, cike da duniyanci ta ce "Amrya ba kya laifi, ko kin kashe ɗan masu gida" jauhar ta zube har ƙasa ta gaisheta. "Lafiya ƙalau, zauna a kan kujera mana jauhar" ta sunkuyar da kai tare da girgizawa ta ce "Nan ma ya isa" "Amira matar Aminu ce fa, kawo mata ruwa dan Allah" kallon banza ta yi wa jauhar, ta gyara zamanta ta cigaba da danna waya. Rahila ta ce "Ke fa 'yar wulaƙanci ce amira". Jauhar ta ce "Ai a ƙoshe ma nake" "Allah sarki, ya mijin naki, tun da aka yi auren ba ki zo mana ba" tayi shiru tare da sunkuyar da kai tana murmushi. "Bari yanzu babansu zai shigo, sai ku gaisa". Amira ta saci kallon jauhar, kyakywar bafulatanar yarinya, daga muryarta kawai zaka san ba ta da hayaniya, ita aka aurawa Al'amin. Abbu ne yayi sallama suka amsa masa gaba ɗaya, ko da ya shigo sau ɗaya jauhar ta kalle shi ta mayar da kanta ƙasa, babu in da Al'amin ya bar kamanin mahaifinsa. "Abbu ga 'yar ka fa, sirikarka matar Aminu" Ya ce "Subhanallah" ya zauna yana faɗin "Yarinyar kirki, tuba nake yi yakamata ace na zo gidan naku, tafiya ta kama ni ne, ina ga yau kwanana huɗu da dawowa, kuma ina maganarku sosai wallahi, dan Allah ki yi haƙuri" "A'a babu komai, ai mu ne masu laifi, tuntuni yakamata ace mun zo, ban san gidan nan ba ne shiyasa shi kuma bai kawo ni ba" Rahila ta ce "Hmm, dama ya za ayi ya kawo ki, ai ko za a shekara sai idan rashin mutuncin sa ne ya kawo shi" yanayin maganganun da rahila tayi, ya tabattar mata da ba ita ce mahaifiyar Al'amin ba. Abbu ya ce "Ina fatan dai ba wata matsala, ba yayi miki wani abu na rashin kyautatawa?" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Ba ya yi mini sai dai.." sai kuma ta yi shiru. Rahila ta yi farat ta ce "Sai dai me, ki faɗa ba wani abu, ai mu duk iyayenku ne". "Ƴan sanda ne suka zo mana cikin dare, suka kama shi suka tafi da shi, naje na kuma zuwa anƙi sakinsa, wai suna zarginsa da ta'amalli da hodar iblis". Rahila ta ce "Taɓ! Ki ce shi likkafa ce ta cigaba a harkar shaye-shayen har ya kai wannan matakin?" Jauhar ta ce "A'a ba ya amfani da ita, wani ne ya kawo ya ce a ajiye masa, ban san kowaye ba, su kuma suka zo amma wallahi ba shi da laifi, shi ne na ce bari na zo, dan Allah baba ko da hanyar da za a bi a sako shi, ba ma shi da lafiya wallahi, da na je dukansa suke yi, jikinsa duk shaidar duka" ta ƙarasa maganar tana kuka, duk yadda ta so riƙe hawayen amma abu ya gagara. Rahila ta ce "Au dama shi ne dalilin zuwan naki? Sai da matsala ta afku ki ka nemi gidan ubansa, in dai wannan ne ya saba, kina zaune 'yan iskan da suke bashi goyon bayan yin rashin mutunci za su saka a sake shi". Abbu ya ce "Ya isa haka rahila" ya kalli Jauhar ya ce "Ki daina kuka yarinyar kirki, case da ya haɗa da irin wannan case ne babba ba ƙarami ba, Al'amin ba ya jin magana ko kaɗan". "Wallahi baba ba shi ya kawo su ba, ban taɓa ganinsa da ita ba". "Idan ma yana ta'amalli da ita, ba gaya miki zai yi ba ai" Abbu ya ce "Ki kwantar da hankalinki, idan da wata matsala ki koma gidanku, zuwa lokacin da komai zai daidaita, zan je na ga abun yi" "Abbu ka san cocaine kuwa? Wallahi ka je suka fuskanci belinsa ka ke son yi, za su iya haɗawa da kai, ka dai koma gefe ka taya su da addu'a, duk masifar da ya janyo ta ƙare masa a kansa idan yana da rabo ya fito, idan babu ya ƙarata a can". Kalaman rahila suka yi wa jauhar zafi da nauyi, ba shiri ta tashi ta ce "To bari na tafi sai anjima". Rahila ta ce "Ki je gida ki yi ta addu'a, idan babu dama ki koma gida, amma shigar mahaifinsa wannan case ɗin ba mafita bane ba, kina zaune za a sako shi". Abbu ya ce "Ki yi haƙuri kin ji, zai fito in sha Allah, zan san abun yi" "Ka daina saka mata rai da zaka yi wani abu fa, haka kurum wani abu ya sameka gani ga 'ya'ya ka barmu" Bayan tafiyar jauhar, Abbu ya ce "Rahila, anya ban yi wauta ba da na biye miki aka aura wa yarinyar mutane Al'amin ba, kalli yadda take cikin tashin hankali da damuwa fa". "Wannan yarinyar fa da ka ke gani, ba a bar tausayi ba ce ba, ko ka manta kangarewa iyayenta ta yi suka nemi maraba da ita?" "Duk da haka rahila, ni fa tantama nake yi a kan maganar nan, gaskiya ina ga zan jagoranci raba auren nan, Al'amin ba zai yi hankali ba" "Abbu ina ruwanka, dan Allah ka bar maganar yaran nan" Jauhar kuwa bayan ta fita, ba tare da tunanin komai ba, ta nufi unguwar su, ta je ta samu baba, ko da wani abu da zai iya taimaka mata, ba tare da tuna haɗarin da hakan ka iya haifarwa ba, kodayeke wanda yake cikin ruwa ko takobi ka miƙa masa kamawa zai yi. Ayshercool 08081012143 28 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci?? Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba?? Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta?? Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki. Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Sosai take sauri, tare da fatan Allah ya sa baba yana nan. Sai dai tayi iya ƙoƙarinta wurin daidaita nutsuwarta, kafin ta ƙarasa gidan. Yamma ta fara yi, yaran gidan sun dawo, sun yi kaca-kaca da shi, duk sun zubar da kayan makarantar su ko ina, ga uban wanke-wanke da aka rasa mai zaman kawar da shi daga wurin. 'yan ƙananan yaran gidan ne suka fara murnar ga jauhar, ɗakin mama ta shiga suka gaisa, ta kalleta ta ce "Lafiya na ganki yanzu? Wani abun ne?" Jauhar ta ce "Lafiya ƙalau wurin baba na zo". "In ce ko dai lafiya, kuma ya san kin zo? Ki tashi ki tafi kar ki saka makakken mijinki ya zo yayi mana tijara da tashin hankali" Anty ce ta leƙo falon ta ce "Jauhar ashe abun da ya faru kenan?" Jauhar ta kalleta ta ce "Anty dama kina nan ina wuni?" "Lafiya ƙalau, ashe kuma kama mijinki aka yi da hodar iblis, abu bai yi daɗi ba". Dammm! Ƙirjin jauhar ya buga, yaya aka yi anty ta san wannan zancen, mama ta ce "Kamar yaya?" "Yanzu muka yi waya da rahila, ta ce bata daɗe da barin gidan ba, ta je musu wai an kama shi". Wani abu ɗaci ya tsaye wa jauhar, kamar ta fashe da kuka, ta ce "Ba ya ta'amalli da hodar iblis, rigima ce kawai ta haɗa su da wasu, shi ne dai na je na sanar musu, kar ya zamana ba su sani ba" "Dan ubanki ni zaki yi wa ƙarya dan ki kare mijinki, ai rahila ba zata yi miki ƙarya ba" Walida ta ce "Taɓ, Allah ya kiyashemu taɓewa, hodar iblis abun ba arziki ai na zata a sara suka kawai ya tsaya ashe babban kai ne" Duk yadda ta so ta riƙe hawayenta ta kasa, ta fashe da kuka, suka din ga aibata Al'amin, gashi ba ta tarar da baba a gida ba, babu alamar za su tausaya mata, ko su rarrasheta, kawai ta tashi ta ɗauki jakarta tana kuka, ta fice. Hafsa ta ce "Allah sarki jauhara da tuni ana china ko gidan Alhaji mu'azzam ana shan A.C" suka din ga dariya. Ta kwashi ƙafa ta nufi gida, tare da ƙudirce wa ranta da yardar Allah, babu abin da zai saka ta sake zuwa gidan nan da matsalarta, ƙarshen ƙiyayya da tsana dai ana nuna mata a gidan nan. Kamar daga sama ta ji an buga mata tsawa "Ke bamu hana ki shigowa unguwar nan ba?" Sai a lokacin ta tuna abun da ya faru, cikin tsoro ta kalli mai yi mata tsawar, sai dai ta kasa magana, ta bishi da ido. "Ba magana nake yi ba" "Nawa ubanka ya bayar aka shimfiɗa unguwar da za a hanata shigowa mahaifarta?" Ta ji wata muryar daban. Ta kalli matashin yaron, guduma kenan ɗan gidan mai unguwa, da su Walid suka bawa ragamar kula da gidan Al'amin da shige da ficen jauhar, har ta je gidan su Al'amin ta taho nasu gidan yana biye da ita. Saroro ta yi tana kallonsa, dan ba ta san shi ba. "Waye kai? Meya kawo ka unguwar nan?" Guduma ya nuna masa Jauhar, ya ce "Wannan, wallahi kana taɓa ta zamu ɓalla ƙarfe a wurin nan, mu rabu salin alin" ɗayan ya ja da baya ya basu hanya, guduma ya ce wa jauhar "Mu je" Ita dai ba ta iya yi masa magana ba, ta cigaba da tafiya ita yanzu gaba ɗaya hankalinta da lissafinta yana kan halin da take ciki a yanzu. Misalin ƙarfe uku da rabi na dare, jirginsu ya sauka malam Aminu Kano international airport, direba ya zo ɗaukarsa. Duk da a gajiye yake, saboda doguwar tafiyar da ya yi, hankalinsa da lissafin sa yana kan, ya ƙarasa gida garin Allah ya waye, ya je ya ji ba'asin dalilin fasa aurensa da yarinyar da ya ƙallafa rai a kanta, kullum cikin tunanin ta yake, kuma tun da aka ce, an fasa bashi ita, ya ji ya ƙara ƙaunarta, ta shiga ransa fiye da yadda yake tunani. *** Kwanaki kaɗan ya rage jauhar ta fara jarrabawa, amma ba ta iya karanta komai, ga uniform ɗin ta, ga litattafanta sai dai ba ta da nutsuwar da za ta yi karatu, duk ta ƙare tayi rama ga rashin abinci dama damuwar da take ciki ba ta barinta ta ci abincin. Walid sai da yayi mata faɗa a kan zuwanta gidansu ba tare da saninsu ba, tare da jaddada mata mugunta da gaba mai tsanani da take tsakaninsa da Al'amin. Tana kwance a falo, maman halimatu ta shigo gidan, ta tarar da ita a kwance cikin damuwa ta ce "Jauhar, rayuwa za ta yiwu a haka kuwa? Yanzu da mutuwa yayi ba dole ki yi haƙuri ba, kin addabi kanki, kamar ko abinci ma fa ba kya ci" kamar ta soso mata wurin da yake yi mata ƙaiƙayi, ta hau rera kuka, ta zauna ta rungume ta ta din ga rarrashinta. Ta ce "Sako hijjabinki mu je gidana, kya ɗan sake ki sha iska, zaman kaɗaicin nan ba abun da zai amfana miki sai ɓacin rai" Haka ta bi maman halimatu, dan ba ta da wani zaɓi face hakan, ta zuba mata abinci ta bata, sai dai ta cakala ta bar shi ta ce ta ƙoshi. Halimatu ta zauna kusa da ita ta ce "Anty jauhar dan Allah ki daina kuka, zaki yi rashin lafiya " tayi maganar tana goge mata hawaye. Akwai shaƙuwa sosai a tsakanin jauhar da yaran layin, wasu ma ko iyayen su ba ta sani ba, amma su tana hulɗa da su, ta yi wa matan kitso, ta koya musu karatu idan tana da abinci ta ba su, ko 'yar alewa ko abun kusa da baka, shiyasa suna son taruwa a gidan idan master baya nan, sai dai rashin walwala da ba ta yi yanzu ya sanya duk suka watse suka daina zuwa. Baban su halimatu ya dawo, dama juahar na tsakar gida, ta gaishe shi ya amsa sama-sama, ya shige falo, ya fara ƙwalawa salamatu kira. "Baban halimatu sannu da zuwa " "Me matar mutumin nan take yi mini a gida? Haka kurum da tsinannen kwashe-kwashenki, ki janyo mana masifa muna zaman lafiya" Cikin takaici ta ce "Haba dan Allah, menene a ciki, tana zaune ita kaɗai cikin damuwa shiyasa na ce ta shigo, amma ka san haka kurum ba mai shige-shige ba ce ba". "Ke ki ka sakata a damuwar da zaki cirota, ambulance uwar taimako " Jauhar na jin su sama-sama, ta tashi ta ɗauki mukullin gidanta, ta fice ta koma gida. Jauhar ta kama addu'a iya yin ta, su liti fafur sun ƙi gaya mata kotun da ake yi wa Al'amin shari'a, kuma suka ƙi gaya mata prison ɗin da yake. Baba yana karyawa da safe, ya ga kiran waya da baƙuwar lamba, ya ɗaga ya ɗan yi gyaran murya yayi sallma. "Wa'alaikum Salam, barka da safiya baba". "Yauwwa barka dai, da wa nake magana?" "Alhaji mu'azzam ne baba, ina ƙofar gida na zo, na ce Allah ya sa ba ka fita ba". Jikin baba yayi sanyi, ya ce "Ahh ina nan ban fita ba tukuna, ashe ka dawo" "Eh baba na dawo" "To gani nan" Ya miƙe zai fita, mama ta ce "Ina zaka kuma kai da waye?" "Baƙo" ya bata amsa a taƙaice. Ya fita tsakar gida, hafsa ta shirya za ta tafi makaranta ya ce "Ke haryanzu baki tafi makarantar ba me ki ke yi?" "Ba ni da lectures ne da wuri, shiyasa yanzu zan tafi" "To Allah ya tsare" ta amsa da amin. Baba ya fito suka gaisa, ya ce "Malam mu'azzam ka dawo ashe?" Cikin girmamawa ya ce "Eh baba, na sameku lafiya?" "Alhamdilillah" "Masha Allah, baba tun ina china na samu wani labari, hankalina duk bai kwanta ba, na yi iya ƙoƙarina wurin dawowa, baba ko wani laifin na yi ka hana ni auren jauhar?" Baba ya girgiza kai ya ce "Wallahi ko ɗaya, kawai dai ka san matar wani ba ta auren mijin wata, Allah bai ƙaddara aurenku ba, ina mai baka haƙuri, na yi maka laifi ban kyauta ba, da kuɗin aurenka a hannuna na aurar da ita, amma ka yi haƙuri dan Allah" A razane ya kalli Baba ya ce "Aure aka yi mata?" Baba ya jinjina masa kai a sanyaye ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" Hafsa kuwa har ta sako kai za ta fita, ta hango Alhaji mu'azzam, ta koma cikin gidan da gudu, ta samu mahaifiyarta a ɗaki ta ce "Anty, saurayin nan na jauhar ne ya zo, Alhaji mu'azzam gashi can da baba a waje" A sukwane ta tashi ta ce "Haba dai?" "Wallahi da gaske nake" "To maza ɗauko kayayyakin nan ki yi amfani da su ki fita kafin ya tafi" Can kuwa Baba sai haƙuri yake bashi, yana yi masa nasiha, dan shi bai san ma an yi mata aure ba sai yanzu, gaba ɗaya ya shiga damuwa, aƙalla zai bawa jauhar shekara ashirin da wani abu, ya girmeta nesa ba kusa ba, sai dai ta shiga ransa sosai da sosai, duk da ya sha yinƙurin ƙara aure a baya, amma matarsa tana hanawa, bai taɓa shiga damuwa na rashin wata ba sai jauhar, kamar ya zubar da hawaye haka yake ji. Jiki a sanyaye ya ce "Shikenan baba babu damuwa, na gode sosai da sosai, Ubangiji Allah ya basu zaman lafiya da zuriya ɗayyiba". Baba ya amsa da "Amin" Suka yi sallama, ya shiga motarsa amma ya kasa tuƙin, ya kifa kansa a sitiring motar, yayi shiru ya ji gaba ɗaya duniyar tayi masa wani iri, babu irin zargin da bai kawo a ransa ba, na dalilin hana shi auren jauhar. "Malam ya dai" da sauri ya ɗago kansa ya ce "Jauhar" "Ba ita ba ce, yayarta ce, tun ɗazu na ganka a nan baka tafi ba, lafiya?" "Yauwwa Alhamdilillah, dan Allah in tambayeki mana?" "Ok, Allah ya sa na sani" tayi maganar tana sake gyara tsayuwarta cikin iyayi. "Ko kin san dalilin da ya saka aka fasa bani aurenta, tun da kin ce ke yayarta ce" "Eh to, rashin ji ta fara yi, baba ya yanke shawarar aurar da ita kawai, tun da baka nan" Alhaji mu'azzam ya ce "Wani irin rashin ji?" "A tunaninka wane rashin ji mace za ta yi, a aurar da ita babu shiri?" Cikin matsanancin mamaki ya ce "Jauhar ɗin?" Hafsa ta ce "Ita fa, ko dan kana ganinta a haka? Dama ba sonka take yi ba, akwai wani saurayinta ɗan daba, da ta ƙallafa rai a kansa, ta fara rashin ji, kawai baba ya aurar da ita, ai ka ga ba zai gaya maka haka ba" yayi shiru yana kallon hafsa, kawai ya ji maganganun nata ba su shige shi ba, ya gyaɗa kai ya ce "Shikenan, Allah ya basu zaman lafiya" Ta ce "Amin, dan Allah ko zaka sauke ni a hanya, school zan tafi ko a titi ne sai na sauka na samu abun hawa?" Ya ce "Bakomai bisimillah" Jauhar ta idar da sallar la'asar, ta ga kiran walid a wayar Viper, ta tashi ta ɗaga da sauri, suka gaisa, ya ce "Wani tunani na yi, akwai uban gidansa da muke yi wa aiki, ɗan majalisa ne, sai dai Viper ne kawai yake iya samunsa kai tsaye, na ce ko wurin P.A ɗin sa zamu je, ki gaya masa dan ni ba shiri muke yi da shi, na taɓa marinsa idan mu ka je da ke wataƙila su saurareki". Cikin ɗoki ta ce "To shikenan, Allah ya sa dai su fito da shi ɗin" ya amsa mata da amin. Hafsa kuwa cike da salo da kisisina, da tasirin sihiri, sai da ta karɓi lambar Alhaji mu'azzam, har bakin department ɗin su ya kaita, sai dai idan zai yi mata magana sai ya kirata da jauhar, sai dai hakan bai dameta ba, lambarsa kawai da ya bata, ya sanya ta din ga jin kamar ta ma riga ta aure shi an gama. Tun safe jauhar ta shirya, ya din ga kiran wayar Walid da ta liti, amma ba ta shiga, tun tana saka ran za su zo, har ta fara sarewa, sai azahar walid ya zo, kamar ta yi masa kuka ta ce "Tun safe nake kiran wayarku, ina jiranka amma shiru ba ta shiga" Walid ya ce "Ai wayar nan ta sa ma kawo ta zaki yi" Cikin mamaki ta ce "Saboda me?" "Akwai dalili, yanzu idan kin shirya ki zo mu je can wurin P.A ɗin ki gaya masa, da mun je shiga zaki yi, mun gama magana da wani yaronsa" ta ce "To" Suna tafe tana yi masa magiyar, dan Allah ya kaita ta ga master, amma ya ce "Shi fa ya ce kar a kuskura a kai ki, yanzu idan muka kai ki tijara zai yi mana". Cikin damuwa ta ce "Haushina yake ji, ba ya son ganina ko?" Ya ce "Gaskiya ba na ce ba, ya ce dai kar a kuskura a kai ki, kuma ranar Litinin zaku fara jarrabawa, ki je ki fara" Mamaki ne ya kama ta, ya aka yi ya san lokacin da za su fara jarrabawa? Tayi ajiyar zuciya ta ce "To yaya jikin sa ya warware?" Walid ya ce "Eh ya warke" "Ina nan ina ɗan haɗa 'yan kayayyakin abinci, sai in baka ka kai masa" "Kar dai ki takurawa kanki" Jauhar ta ce "Ban takura kaina ba, amma dan Allah idan ka je ka ƙara bashi haƙuri, wallahi laifina ne ban gaya masa an kawo abun ba, kuma mantawa na yi" Ya ce "Manta kawai, dama Allah ya riga ya ƙaddara faruwar hakan". Suna zuwa ofishin, ba su wani sha wahala ba, aka shiga da Jauhar, ta gaishe shi ya amsa mata, ya ɗan ƙare mata kallo ya ce "Kamar na taɓa ganinki" Jauhar ta ce "Eh, akwai ranar da na je wurin mijina, na tarar ka je kai da yaya walid an fito da shi a police station". "Oh matar mai zamani ce, Viper?" Ta jinjina masa kai ta ce "Eh nice" Ya ce "Allah sarki, ya gida ya fama da rigimammen mijinki" Tayi murmushi tana wasa da yatsun hannunta. "Yaya aka yi?" Jauhar ta sauke numfashi ta ce "Dama, mijin nawa aka kama, har an kai shi prison an ƙi sakinsa, shi ne na ce bari na zo wurinka dan Allah ko zaka yi wa honorable magana, ko za a fito da shi" Ya girgiza kai ya ce "Al'amin ba zai canza hali ba, me kuma yayi a wannan karon?" "Ba laifinsa bane, abu aka kawo aka ce na ajiye masa, ban san ko menene ba, kuma na manta ban gaya masa ba, jami'an tsaro suka zo suka yi bincike cikin dare, suka kama shi, wai sun ga hodar iblis a cikin kayan" Cikin mamaki ya ce "Hodar iblis kuma? A ina ya sameta?" "Ai ba shi ne ya kawo ba, ba ya ta'amalli da ita" "Taɓɗijan, a wannan karon case ɗin babba ne, bari na kira honorable duk da ba ya gari". Ya kira honorable Indabo, ya sakata a hansfree tana jin duk abun da suke faɗa, suka gaisa. P.A ya ce "Honorable, mutumin ka fa ya janyo babbar jagwal ga matarsa nan a gabana ta zo a taimaka mata a fito da shi" "Wa kenan?" "Ma dogon zamani mana" Indabo ya ce "Kuma dai? Me kuma yayi?" "To wai hodar iblis ce, aka kama shi da ita?" "What! Coacine? Yaron nan yana da hankali kuwa, a ina ya samu coacine kuma?" "To ina zan sani, matarsa dai ta ce ba laifinsa bane ba" "Please count me out of this please, haka kurum na je fito da shi, 'yan adawa su sami na yi mini yarfe, ace nima safararta nake yi? Dama dai wani rashin jin yayi ba wannan ba, ni fa dama Saboda aikina na cin zaɓe siyasa dole sai da irinsu, shiyasa nake fito da shi, amma ban da haka meye haɗina da shi, zan nemi wani ya cigaba da yi mini ayyukana ni babu ruwana" P.A ya ce "A'a honorable, wani kaya fa sai amale, wallahi ba kowane matashi ne yake da ƙwarin da yake da shi ba, kar ka yar da shi wani ya ɗaka" "Ka san dai yanzu bana gari ko, dan Allah ka bar ni, ni yanzu lissafin siyasata na saka a gaba, idan ina buƙatar sa a gaba, na fito da shi" ya kashe wayarsa. P.A ya kalli Jauhar da jikinta yayi sanyi, mamaki ya cika mata kai da zuciya, wato yana amfani da jini da lafiyar Al'amin ne kawai dan cimma nasa burin, abun ya bata mamaki sosai da sosai. "Madam, kin ji abinda honorable ya ce, amma ki yi haƙuri zuwa ya dawo, mu gani zan cigaba da lallaɓa shi, kar ki damu da abubuwan da ya faɗa, kansa ne ya ɗauki zafi, amma shi da Aminu ba ta ɓaci, in dai wannan harkar ce, ba shi da sama shi". Ba ta ce masa uffan ba, ta tashi ta fita, yanayin yadda ta fito ne, ya tabbatar masa da akwia matsala. Ya ce "Yaya? Wani abun yayi miki ko maganar banza yayi miki, na shiga na ci ubansa" Ta girgiza masa kai alamar a a. "To meyafaru?" "Honorable ɗin ya ce babu ruwansa, ba zai shiga maganar ba saboda kar sunansa ya ɓaci" tayi maganar hawaye yana gangarowa daga idanunta. Walid ya yi shiru, tare da jinjina kai ya ce "Shikenan, bakomai mu tafi" Haka suka tafi duk jiki a sanyaye, ta ce "Yanzu shikenan babu abun da za ayi? Haka zai cigaba da zama?" "A'a zai fito, haryanzu ba a gama shari'ar ba ma, dole za a nemi wata hanyar". Jauhar ta ce "To shikenan, dan Allah ranar juma'a ka zo ka karɓi kayan da na tara, sai ka kai masa". Walid ya ce "Shikenan, in sha Allah, amma kar ki je ki saka damuwa a ranki, idan da wata matsala, ki kira ni a wayarki" Ta girgiza kai ta ce "Bani da waya" "To ki ara a ta maƙwabta, barinki da wayarsa akwai matsala, haka ya karɓe wayar Viper ya tafi da ita. Ta cigaba da faɗi tashi, wasila ta din ga aiko mata da abinci, sai dai sam jauhar ba ta son hakan. Aka fara exams, sai dai ba ta iya mayar da hankali wurin yin wani abun kirki, wataran kuɗin motar ma gagararta yake yi. Sai dai tana iya ƙoƙarin ta wurin aro jarumta, da ɓoye damuwarta, idan ta shiga cikin 'yan uwanta ɗalibai. Sannu a hankali ta fito daga harabar makarantar, ta tarar da yaya saifu. Murmushi ta yi ta ce "Yaya saifu, kai ne?" Ya ce "Eh, hau babur ɗin na kai ki gida" cikin murna ta ƙarasa ta rirriƙe shi ta hau, ta ce "Na zo gida sau biyu ban same ka ba". "Yau ai gani, mu je gidan naki". Ya ja babur ɗin, ta ce "Allah ya sa ba laifi na yi maka ba, na ganka kamar ranka a ɓace". Yayi mata shiru, suka ƙarasa gidanta, ta buɗe musu suka shiga. Ta kawo masa ruwa a jug, dan na rijiya yanzu take sha, ko kuɗin sayen ruwa ba ta da shi. "Waliyiyya" "Na'am yaya saifu" "Meyafaru da mijinki?" Tayi shiru ta ƙi magana. "Ki yi mini bayani ina jinki" Kawai ta fashe da kuka, yayi mata shiru tayi mai isarta, ya koma kusa da ita ya zuba mata ido ya ce "Jauhar, wani irin zama ki ke yi a gidan nan, na san akwai ƙalubale da ki ke fuskanta a gidanmu, amma atleast ai ko ni kya gayawa, sai ji na yi ana zancen an kama shi da cocaine, a tsakar gida ko baba ba ma bai sani ba, da yaya ki ke rayuwa ke kaɗai? Da yaya ki ke samun abun da za ki ci?" "Yaya saifu, ni cin abinci ko akasin haka bai dame ni ba, fatana da burina ya fito, ba shi da laifi, ko a yaya yake na yadda shi Allah ya zaɓa mini, ba ya dukana ba ya zagina. Ban san dalilin da ya sanya su mama suka zaɓi na aure shi ba, na karɓi ƙaddarata, na je gidan ai, amma yanayin karɓar da na samu na san ba zan yi nasara ba, kuma ban ma samu baba a gida ba". "Jauhar, a raba auren nan, ni ban ga alamar za a samu ɗa mai ido ba a auren nan ba, rannan fa cewa aka yi sai da ya zo ya tafi da ke, 'yan daba za su saraki, wace irin rayuwa ce haka? Ko khul'i ayi a raba auren nan" Tayi shiru ta sunkuyar da kanta. "Yaya ki ka yi shiru? Ko kina son shi ne?" Ta girgiza masa kai alamar a'a. "To kin amince a raba auren?" Nan ma ta girgiza kai. "Ki yi mini magana jauhar, idan kin amince in yi wa baba magana, a raba auren nan" "Dan Allah kar a raba, ni dai a fito mini da shi dan Allah" Saifu ya ce "Wai son shi ki ke yi ne?" Cikin kuka ta ce "Idan aka raba auren za ace mini bazawara" "To a kanki aka fara? Ba sai ki koma makarantar ki ki yi a tsanake ba?" Ta girgiza kai ta ce "Dan Allah ni dai yaya saifu kar a kashe mini aure, duk abun da yake yi zai daina a hankali, sharri ake yi masa ba ya ta'amalli da hodar iblis" saifu yayi shiru yana kallon ta, ya fara tunanin any ba son shi take yi ba, ya ma kasa gane me take nufi. "Shikenan, ƙyale baban ma, yanzu da an yi magana da shi, sai ya gaya wa matansa, wace kotun ake yi masa shari'a? Akwai wani baban abokina, sai na yi wa abokin nawa magana a san abun yi" Cikin murna ta ce "Na gode sosai yaya, ban san wace kotun ba ce ba, wai ya hana a kai ni, amma akwai lambar abokinsa, da tare muke up and down, ka ga daga nan ma sai mu je na ganshi". "No, tun da ya ce kar ki je, ba sai kin je ba, duk abun da ake ciki, zan din ga sanar miki, amma ki kwantar da hankalinki dan waliyiyya, tun da kin na ce, ke uwar soyayya Allah ya bar ƙauna, amma wallahi na tsani mijin nan naki" Ta ce "Dan Allah ka daina faɗa, ba zan ji daɗi ba, a din ga yi mana addu'a, ba na jin daɗi idan aka aibata shi" Ya ce "Iyee lallai waliyiyya baki ya buɗe, ki na so dai ki gaya mini ki na son mijinki maybe ma fiye da ni, to wallahi ki fi so na a kansa" Ta ɓoye fuskarta tana dariya ta ce "Wallahi yaya tausayi yake bani kawai, idan aka raba auren nan, akwai damuwa, kuma ina saka ran komai zai zama tarihi in sha Allah" Ya ce "Tafi can, kya ma faɗi gaskiya, kuma ko ba yau ba, kar ki sake wani ma ya san na shiga maganar nan, ai mu na da alfarma shige-shige yayi mana rana" jauhar tayi murmushi, ya bata kuɗi ya tafi. Kusan sati ba ta ƙara jin ɗuriyar saifu ba, ga babu su walid balle ta ji wani abu daga gare su, sai da ta ari wayar wasila, ta kira walid ta ce ya zo ya karɓi kayan da zai kai wa master. Ta saya masa maggi, mai, da sauran ɗan abun da ba a rasa ba, da prisoner zai buƙata. Ya karɓa tare da ƙara bata haƙuri, da ba ta tabbacin, yana nan suna ƙoƙarin fitar da Mijinta. Saifu ya sake komawa makaranta ya sameta, cikin murna ta hau tambayar sa, ya ake ciki?. "Ke mijinki abun da aka yi masa shiri ne kawai, na bibiyi abun ni da abokina, zaki sha mamaki idan na gaya miki an yi wani mugun sara a kan gaɓa, amma ba zan gaya miki ba, in je zaƙin soyayya ya ja ki ki gaya masa ba idan ya fito, ki haddasa husuma, baban abokin nawa yayi magana, sun ce ayi haƙuri ya ƙarasa wata ɗaya, kotu za ta wanke shi ya fito, ashirin da biyu ga watan gobe za a sake shi" "Wayyo Allah, yaya saifu kusan watanni uku fa kenan zai yi a prison?" "Au baki gode ba kenan?" Jiki a sanyaye ta ce "A'a na gode sosai yayana, Ubangiji Allah ya saka maka da gidan aljanna, to zaka kai ni na ganshi?" Ya ce "Amin ya rabb, yana prison na ciki gari, kuma ban ce ki je ba, kar ki kuskura ki je, kin ji na gaya miki" "Amma yaya meyasa?" Saifu ya ce "Saboda haka na ce miki, kuma ke ma kin ce ya ce kar ki je, kar kuma gaya wa wani gashi zai fito shi ma bai sani ba". Jauhar ta ce "To shikenan, na gode Allah ya saka maka da mafificin alkhairi" "Amin ki koma gida, ki cigaba da exams ɗinki, idan da wani abu, ki neme ni a waya, kar ma ki sake zuwa gidan nan da wani batu a kan aurenki, tun da ki na son abun ki ki yi zamanki" Tayi murmushi ta ce "Ban san menene son ba dai yaya, ban san me ake ji ba, da farko dai na san ina jin tsoronsa sosai, amma yanzu kuma tausayin sa nake ji" Yayi murmushi ya ce "Ga kuɗin mota, ki sauka lafiya, yau ba zan je gidanki ba" Ta karɓa cikin murna tayi masa godiya, ta tafi gida. Ta ji sanyi a ranta jin cewar zai fito, sai dai tana cikin damuwa na rashin sanin halin da yake ciki, ya ji sauƙi ko kuwa, yana samun abinci ko kuwa?" Da ta samu kuɗi, take yin sayayya, ta ari waya ta kira walid, ya zo ya karɓa ya kai masa. Sana'a tuƙuru jauhar kamar tayi ƙwace, dama ga azumi yana gabatowa, ana samun ɗinkuna, dan haka tana samun aikin stone da beads, sai dai ba ta iya sakin jiki ta kashe kuɗin, saboda akwai abun da take son yi. Ita ce mayafai, har da su kantu da aya,  haka take saya ta soya ta ɗaura a leda yara na saya. Har guga take karɓar kayan maman halimatu, ta ta da ta yara tayi mata, ta biyata. Sana'oi kamar zata yi ƙwace, duk da ana yi mata mugunta a kan wasu abubuwan, mussman gidan mai ɗinki, da take yi mata aikin stone ta fara yi mata mugunta. Ta ƙara tsananta addu'a, da roƙon Allah, a kan Allah ya kuɓutar mata da mijinta, ya shirya mata shi. Rana ba ta ƙarya, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, saura kwanaki biyu Al'amin ya fito, jauhar ta yi ta gyaran gida, ta ƙara gyara masa ɗakinsa. Ranar da zai fito ɗin, ta yi girki, sai dai kuɗin hannunta ba su da yawa, duk mutane sun riƙe mata kuɗi, dan muɗin hannunta ba za su ishe su kuɗin mota ba ita da shi. Ta dafa ruwa ta zuba a flask, ta shirya tun ƙarfe tara, ta tafi prison ɗin, gashi damuna ta ja baya, an fara wani irin sanyi mai ratsa jiki. Ta nemi shiga cikin prsion ɗin, aka ce mata a waje za ta jira, idan yau za a sake shi, za ta ganshi ya fito. Tana nan zaune, wasu suna ta fitowa, 'yan uwansu suna ta murna, sai dai shiru-shiru ba ta ganshi ba. Nan hankalinta ya tashi, ta sake nufar wurin masu gadin ta ce "Wai haryanzu ban ganshi ba, kuma yau aka ce mini za a sake shi" "Waye ya ce miki za a sake shi?" Wani gandiroba ya tambayeta. "Yayana ne" "Yayan naki alƙali ne? Ko shi ya kawo shi nan ɗin, wanda zamu saki kenan yau sun gama fitowa" "Innalillahi na shiga uku" ta faɗa a raunane. Ayshercool 08081012143 29 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci?? Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba?? Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta?? Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki. Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Da kallo suka bi jauhar, ganin yadda take yi musu kuka wiwi, wani gandiroba ya ce "Koma tsallake, idan ki ka gama kukan, sai ki tafi". Ta juya ta kama hanyar tafiya, tana ji a ranta kamar duk duniya, babu wanda ya kaita rashin sa'a. Sannu a hankali yake tunkaro gate ɗin fitowar, zuciyarsa cike da mamakin yadda aka sake shi, dan bai san ma zai fita ba, sai yau ɗin. Tsayawa yayi bayan ya fito daga cikin gate ɗin, ya lumshe idanunsa sakamakon hasken ranar da ya ji ya yi wa idanuwansa yawa, sannu a hankali ya cigaba da buɗe su, har ya ji hasken yayi dai dai da abun da idon nasa yake buƙata. Kamar an kira sunanta ta waiwayo, ta hangoshi a tsaye, shi ma ita yake kallo da mamaki, ba ƙaramin kashedi ya yi wa su liti ba, a kan kar su kuma ɗaukarta su kaita in da yake. Da sauri ta nufo shi, ta kasa tsayar da hawayenta ta na wata irin ajiyar zuciya ta ce "Har na ji daɗi, da suka ce mini, ba za su sake ka yau ba" Yayi shiru yana kallon ta. Ƙare masa kallo take yi, an yi masa aski an aske masa sajensa da gemunsa, sai ɗan kaɗan da ya fara fitowa, idanunsa sun washe yayi haske, saboda babu kayan shaye-shaye a nan, sai dai ya rame sosai. Kallonta kawai yake yi, kamar wata baƙuwar halitta, sai dai bai yi mata magana ba. Tayi ajiyar zuciya ta ce "Mu tafi?" Ya jinjina mata kai yayi gaba. Ta ɗaga ƙafarta kenan takalminta ya tsinke, ta durƙusa ta cire takalmin ta ce "Takalmina ya tsinke" ya kalli ƙafarta sannan ya dubeta, ƙafarta busu-busu, duk yadda ya santa da gayu, ko ba ta gaya masa ba, ya san tafiyar ƙafa ta yi. Ta tsayar musu da abun hawa suka hau, sai dai har suka je in da za su sauka, duk surutun da take yi, ko sau ɗaya bai tanka mata ba. A titi suka sauka, saboda kuɗin motar ba zai isa a shiga da su har ƙofar layin ba, har ta yi gaba, ya janyota ya cire mata takalmansa ba tare da ya ce komai ba. Ta ce "A'a ka saka kar ka taka wani abun". Kallon da yayi mata, ya sanya ta yin shiru, ta saka takalman kamar zata tashi sama a kansu suka shiga layinsu, kamar ta taka rawa, master ya fito. A falo ya zauna, ya kashingiɗa ya lumshe idanunsa, ta shiga banɗakinsa, ta haɗa masa ruwa mai zafi, ta ce "Master ga ruwan wanka na kai maka" bai yi mata musu ba, ya tashi ya tafi, kafin ya fito ta jera abinci a falo, ya yi wankan ya fito falo, ya tarar da abinci, yanayin yadda yake cin abincin ya tabattar mata da yana jin yunwa sosai duk da dama can acici ne. Yana so yayi mata magana, amma ya rasa me zai ce mata ma, ya gama ci ya tafi ɗakinsa ya kwanta, dan surutunta ya fara takura shi, duk da yayi kewar abubuwa da yawa a tare da ita, sai dai yadda yake jin zuciyarsa a cunkushe babu daɗi, ya sanya shi jin surutunta ya gundure shi. Allah ya taimaketa, ya wuni a ɗaki, bai fita ko ina ba, tun da ya dawo. Hafsa kuwa ta samu abun yi, dan tun da Allah ya sa ta mallaki lambar wayar Alhaji mu'azzam, take kiransa a waya, da sunan rarrashin sa a kan rashin jauhar, tare da ƙoƙarin sake ɓata jauhar ɗin a wurinsa. Mahaifiyarta ta sake miƙewa wurin shige-shige a kan Allah ya tabattar da lamarin aure tsakanin hafsa da Alhaji mu'azzam. Cikin ikon Allah, idan ta kira shi, yana amsawa ba ya yi mata wulaƙanci ko makamancin haka, hakan ya sa ta cigaba da ƙoƙarin cusa kanta cikin hikima da kissa. Sannan suka yi ƙoƙarin rufe wa mama duk wani abu da yake faruwa, ba ta san halin da ake ciki ba. Kasancewar Al'amin ya fito ya dawo gida, ya sanya jauhar yin isashshen baccin da rabonta da shi, tun kan a rufe shi, dan bayan sallar asuba da ta kwanta, ba ta farka ba sai goma saura. Ta fito tsakar gida da sauri, ta fara aikace-aikace, ta dafa tea ta soya dankalin hausa. Ta dafawa Al'amin ruwa a heater, ta je ƙofar ɗakin ta tsaya tana sallama. Ƙasa-ƙasa ya amsa, ban da yana da buɗaɗɗiyar murya ma ba za ta ji ba, ta shiga tana sake yin wata ta ce "Ina kwana master" "Lafiya ƙalau" "Ban san ka tashi ba, yau na makara da na fara kawo maka ruwan wankan ai, bari na haɗa maka" ta haɗa masa, yanzu ma bai yi musun yin wankan ba, ya tashi ya shiga banɗakin. Ɗakin fes yake, amma ta din da karkaɗe karkaɗe, da goge-goge, ta kunna turaren wuta, ta fito masa da kaya ta saka musu turare. Ya gama ya fito, jikinsa yana ɗigar da ruwan wanka, ya ɗauki dogon wando ya saka, ya zube mata wanda ya cire a kan katifa ya fito. Kallo ɗaya tayi masa ta kawar da kanta gefe ta ce "Ba ka saka rigar ba, na fito maka da ita ma". "Ba na buƙata, wandon ya isheni". Jauhar ta ce "To ai kar ayi sallama, a ganka a haka". "Ki koma ɗaki idan ba zaki iya kallona a haka ba" yayi maganar yana zama. Ya kalleta ita ma yau ba hijjabi a jikinta, doguwar rigar material ta saka, mamaki yake yi, yadda ta yi duhu, ga wani uban ƙashin wuya da ya fito mata, tayi rama sosai da sosai, ashe jiya dan ya ganta a cikin hijjabi ne ya sanya bai gane ba, sai ya ji ransa babu daɗi. Ta haɗa masa abincin ta miƙa masa, ya ɗauka zai kai baki ta ce "Bisimillah" a zuciyarsa ya maimaita sannan ya fara ci. "Askin nan da aka yi maka, ka yi kyau, sai dai ban so aka aske gemun ba gaba ɗaya" Idan ba gizo idanunta suka so yi mata ba, da murmushi zai yi ya shanye abun sa. Ta tanƙwashe ƙafarta ta sake cewa "Sannu master, a prison ɗin ma duka ake yi, na ga bayanka duk shaidar duka. Wallahi ba zan taɓa yafewa wanda suka yi maka sharri ba, ban taɓa shiga tashin hankalin da na shiga ba, na san baka ta'mali da wannan abar, sauran ma zaka daina wataran in sha Allah" tayi maganar hawaye na cika mata ido. "Kun kusa gama exams ko?" Jin yayi magana ya sanya ta saurin ce wa "Eh, cikin azumi zamu gama in sha Allah" "Allah ya taimaka" "Amin na gode, baka tambayeni kwaɗinka da ƙadangaru ba?" Ya rausayar da kai ya ce "Ai naki ne ba nawa ba" hakan yayi da kammala cin abincin. Ta ce "Alhamdilillahilazi aɗa'amana haza, warazaƙatana min gairi haulin minni wala ƙuwwa, Ubangiji Allah ya ciyar da mu na anjima" tayi maganar tana tattare kwanukan. Kafin ta dawo ya ɗauki pillown kujera ya kwanta. Ta je gabansa, ta durƙusa ta kai hannunta goshinsa ta ce "Wai haryanzu kana zazzaɓin ne?" Ya girgiza kai alamar a'a. "Master duk ka yi wani iri kamar an canza mini kai" duk lokacin da ta danganta shi da ita, sai ya ji wani abu a ransa da bai san Menene ba. Yana daga kwance ya din ga miƙa, yana ɗan banƙare kafaɗunsa zuwa bayansa. "Ciwo bayanka yake yi ne?" Ya gyaɗa mata kai alamar eh. "Bari na ɗaukko man zafi na shafa maka zaka ji daɗi, naga wani raunin bai gama warkewa ba". Ya jinjina mata kai, sai dai bai buɗe idonsa ba. Ta je ta ɗauko man, ta dawo ta zauna a bayansa, tana shafa masa a hankali. Ta ce "Juyo" ya gyara kwanciyar sa a hankali, jikinsa wasu wuraren duk shaidar yankan wuƙa, bayan tabon duka. Haka kurum zuciyarta ke raya mata, kai hannu kan gashin da yake kwance a ƙirjinsa, da sauri ta rintse idanunta ta kawar da wannan tunanin ta kira sunansa. "Master" "Mmm?" Ya amsa idonsa a rufe. Ta ce "Ka na jina?" "Mmm" A ɗan shagwaɓe ta ce "To ka kalle ni, magana zamu yi fa" Ya buɗe idanunsa a kanta, take ta sunkuyar da kanta, saboda wani irin nauyi da kwarjinin da idanun nasa suka yi mata, a tunaninta ta daina jin tsoron sa, ashe haryanzu da sauran rina a kaba, yayi mata shiru yana kallonta yana jiran tayi maganar, sai dai ta kasa. Gaba ɗaya sai ta diririce, ta kasa maganar sai cigaba da shafa masa man zafi a wuri ɗaya a kafaɗarsa. Hannunsa ya saka ya cire nata, ya karɓi man zafin ya ajiye, ya ce "Ya aka yi?" "Dama sonake na ce dan Allah ka yi haƙuri ka yafe mini, na yi sanadiyar shigarka wahala, duk laifina ne da ban gaya maka an kawo maka saƙo ba, ka yi haƙuri mantawa na yi ka yafe mini dan Allah" "Idan naƙi fa" yayi maganar very serious. Cikin damuwa ta ce "Please dan Allah ka yi haƙuri" "Zan duba, ki je ki yi karatunki saboda exams" ta jinjina kai ta tashi, tsakar gida ta fita ta hau wanke-wanke, ta ɗaukko kayansa da ya cire, da wanda ya dawo da su daga prison, ta jiƙa su dan ta wanke. Wasila maƙwabciyarta ce tayi sallama, kasancewar ƙofar ba a rufe take ba, jauhar ta ce "Anty wasila sannu da zuwa ga kujera" "Yauwwa jauhara, ashe mai house ya dawo, jiya na ji halimatu ta ce ta ganku, na zata sharrinta ne ma, na zo ɗazu tun takwas da rabi, na yi ta bugu baki buɗe ba na ce bari na tafi, su jauhar ana can jikin miji an liƙe ba a tashi ba" Jauhar kawai ta yi murmushi tana fatan Allah ya sa bai jiyo ba, tun da yana falo a kwance. Ta ce "Jiyan ya fito, ban samu na shigo na gaya muku ba ke da maman halimatu". "Allah sarki jauhar, kin sha wahala shikenan kuka ya ƙare, ki daina anty wasila ba ki san me nake ji ba, zuciyata kamar ciwo take, Allah dai ya bar wannan ƙauna, zuciyar ya daina ciwo ko?" Dariya kawai jauhar take yi ta ce "Ta daina" "To ai da kamata yayi, da ki ka san zai fito, ki yi magana ayi gyare-gyare a gyara masa turaka, ki zo na baki kayan maman nihal Anty maryam, na sanmiki kayanta ki gwada ki ji, ai ba kya yi shiru ki zauna haka ba" (Ga mai buƙatar jarraba kayan maman neehal sai ya tuntuɓeta ta wannan lambar 0706 677 4630). Wasila ta din ga sakin layi, sai da jauhar ta ce "Anty wasila yana nan fa, yana falo yana jinki" Tayi ƙasa da muryarta ta ce "Na shiga uku, kuma ki ka bar ni nake ta zuba, amma baki kyauta mini ba". Ta durƙusa ta kwashi takalmanta cikin sanɗa, ta fice, jauhar ta din ga dariya, ta rufe ƙofarta, sai dai ita ma shiga falon ya gagareta, saboda kunyar abun da wasila ta din ga faɗa, dan ta san halinsa, sai ta sakankance, bacci yake yi, ta ga idonsa biyu. Ta jima tana raɓe-raɓe kafin ta shiga ɗakin, baccinsa yake yi, sosai take jin tausayinsa, yanayin yadda yake miƙa ma, kawai ya tabbatar mata da zaman gidan kaso bai yi masa daɗi ba. Tana ta dirzar kayansa, ta ji an yi wani irin fito a waje, sannan aka buga mata gate, ta saka hijjabi ta buɗe ta ga su walid. Ta ce "Yaya walid, ina wuni" "Madam dama mutumin nan ya fito baki sanar mana ba? Sai yaran da muka saka gadinki ne suka faɗa mana". "Dan Allah ku yi haƙuri, na san zai neme ku, bacci yake yi ne". Liti ya ce "Ko dai ki ka ɓoye shi ki ka hana shi fitowa" Ta ce "A'a na isa? Ban hana shi fitowa ba, ina dai roƙon Allah ku bar mini shi, na san dole dai zai zo in da ku ke". Walid ya sake wani irin fito, tana waiwayawa ta ga har ya zira riga ya fito. Saroro ta yi ta tsaya tana kallon sa, ya ƙaraso, zai raɓata ya wuce. Jiki a sanyaye ta ce "Fita zaka yi? Ban gama ganinka ba fa" Kallonta ya yi, ya raɓa zai wuce ta ce "Dan Allah Master kar ka sha komai, ko ka je in da ake aikata laifi, dan Allah" maganar da tayi, har hawaye ya cika mata ido. Bai kulata ba ya fita, gaba ɗaya sai ta ji garin yayi mata babu daɗi, duk da tana cikin shauƙi, da farincikin dawowarsa. Tana jin shewar su walid, da suka ganshi, ta ja jikinta, ta koma ɗaki, aikin ma ta kasa cigaba, kawai ta saka kuka, kasancewar shi ne kaɗai abun da take yi, ta rage damuwarta, sai kuma tsananta ambaton Allah. Tun wannan fitar da yayi, tun tana saka ran dawowarsa, har ta cire rai, dan har magariba ba ta kuma saka shi a idonta ba. Tayi ta addu'a a ranta, Allah ya sa yana lafiya. Har bayan goma na dare, ta kasa kwanciya, sai sha ɗaya da wani abu, ta ji yana rufe ƙofa, ta fito falo da sauri, ya shigo yana haska fitilar wayarsa, gaba ɗaya falon ya gauraye da warin wiwin da yake yi, jikinta yayi sanyi ta kasa yi masa magana, yadda yake tafiya ya tabattar mata da a buge yake, ya wuce ta ya tafi ɗakinsa. Ta nemi wuri ta zauna a wurin, ta haɗa kai da gwiwa, ta din ga kuka ƙasa-ƙasa, ta tashi ta nufi ƙofar ɗakinsa ta leƙa, ɗakin duhu, sai dai tana hango hasken wutar jikin sigarinsa, ta juya ta koma ɗakinta, ta ji tana neman sarewa, kamar Allah ba zai karɓi addu'arta a kan sa ba, da sauri ta din ga istigfari, ta nemi wuri ta kwanta. Da safe da ta tashi, ba ta ko nufi ƙofar ɗakinsa ba, sai da ya fito ya tarar da ita a falo, tana shirin dutse. Cikin girmamawa ta ce "Ina kwana" "Lafiya ƙalau" ya zauna a kan doguwar kujera, ta ce "Afuwan kar ka ga ban kawo komai ba, wallahi ba kuɗi a hannuna ban girka komai ba" Bai yi magana ba, sai kamar bayan mintuna goma, ya ɗauki wayarsa ya ɗan danna ya saka a kunnensa. "Kawo mini bredi da lipton, kayan tea dai na dubu biyu, kawo mini gida ka karɓi kuɗin". Ya ajiye wayar. Jin wayar da ya yi ya sanya ta tashi ta ɗora tea, kasancewar da wuta ta ɗora a heater. Tana cikin kwashe tea ɗin, ya fito ya je ya karɓo kayan shayin, ya ajiye mata a ƙofar kitchen. Ta ce "To, Allah ya saka da alkhairi" Ta ɗauka ta dudduba, da yabi ta ita, iya buredi da sugan ya isa, sauran kuɗin ko taliya sa saya, ta ɗauka ta soya ƙwan, ta kawo kayan karin. Shikaɗai ta haɗawa ta koma gefe, ta cigaba da shirinta. "Wannan shirirtar ta fi ki karya kumallo?" Ta girgiza kai ta ce "Ba na jin yunwa ne, zan karya amma". Gaba ɗaya ba ta walwala,  duk surutun nan ma da take yi masa, yau bakinta shiru, ta kunna mp ɗin ta, ta ajiye a gefe, tana saurar radio, ana ta zancen za a tafi yajin aiki, saboda tsadar rayuwa da rashin ingantacciyar rayuwa ga ma'aikata. "Amm Angela ki ke ko?" Tayi murmushi ta ce "Ko 'yar madara ba" tayi maganar cikin ƙoƙarin ɓoye damuwar da take ciki. "Koma dai wanne ne, magana ce da ni" Ta ce "To" ta ajiye kayan abun da take yi, ta fuskance shi, amma ba ta yadda sun haɗa ido ba. "Kalleni, idan ina magana na fi son ki kalleni, ki daina sunkuyar da kai" Kallo ɗaya tayi masa ta sake sunkuyar da kai ta ce "Ba zan iya ba ne, wani abu nake gani a cikin idon naka da yake bani tsoro" "Kin kusa daina gani, wata shawara na yanke a kan zamanmu, ni wannan yawan koke-koken da ki ke yi, da wahalar da ki ke sha ba na so, jin sa nake yi kamar wani nauyi a kaina, kuma ni gaskiya ba zan iya daina wasu abubuwan ba, ina saka ki a damuwa da matsala sosai, ga rayuwar ki a cikin hatsari, duk saboda ni. Kina takura rayuwata sosai da sosai, nima kuma ma san ina takura ki dan haka na yanke shawarar kawai na sauwwaƙe miki, ki koma gida Allah ya baki wani mijin ki yi aure, ni ba na buƙatar mace a cikin rayuwata". Tun da ya fara maganar, ta ji kamar an jona mata shocking, zuciyarta ta din ga bugawa da wani irin sauri, ta rasa me ma za ta ce. Sai da ya kammala tsaf, sannan cikin ƙarfin hali ta kalleshi ta kawar da mai ta ce "Wannan ne tukuicina kenan? Baka buƙatar mace a rayuwarka, nima ƙaddara ce ta kawo ni in da ka ke, na zata idan na jure na cigaba da yi wa baba biyayya, na yi biyayyar aure, komai zai wuce, zan ci riba, amma yanzu na fuskanci ni ce mara sa'ar, ko ina ba a buƙata ta,  yanzu tozarta maraicina shi ne ka ga ya dace da ni, har ya sanya ka ce ba zaka yafe mini ba jiya? shikenan ka bani a rubuce na kai wa baban, na gode master, amma duniya da ba a yafiya da mu zo i yanzu ba, na san nayi maka kuskure amma na baka haƙuri, amma ka sani idan ka sake ni, ka tozarta maraici" ji tayi numfashinta ya yi wa ƙirjinta nauyi, kawai ta tashi jikinta na rawa. Tsananin fargaba da tashin hankalin maganar da ya gaya mata, ya sanya period ya zo mata ba shiri, har jikinta ya ɓaci, dama sauran kwana ɗaya ya zo. Har tayi maganar ta gama, ba ta kalleshi ba ko sau ɗaya. A ransa ya din ga maimaita ;idan ka sake ni, ka tozarta maraicina. Ita a tunaninta abun da ya faru ne ya sanya ya ce zai rabu da ita? Marainiya ce kenan? Ya tambayi kansa a lokaci ɗaya ya bawa kansa amsa da no wonder. Sai kuma jikinsa yayi sanyi, shi wannan wahalar da take sha, ya ɗauka za ta yi murna da abun da ya ce, kawai ya basar ya kwanta. Sosai ta din ga kuka, a ɗakinta, tana tunanin wane irin baƙin jini ne da ita haka? Duk yadda take haƙuri tana lallaɓa auren nan, amma ya yi mata wannan sakayyar, take ta fara tunanin wane irin zama zata koma ta yi a wannan gidan na su, da suke nuna mata ƙiyayyarsu a fili? Da ƙyar ta shiga banɗaki ta gyara jikinta, ta fito zauna a ƙasa ta cigaba da kuka. Bayan ya gama abun da yake yi, ya fice ya bar gidan. Kanta ne ya fara ciwo, ga numfashinta da yake ta barazanar ɗaukewa, ga wani irin azababben ciwon mara da yazo mata da zazzaɓi duk a sanadin tashin hankalin maganganun Al'amin. Yaya saifu kuwa tun da ya dinga bibiya, aka tabattar masa da an saki Al'amin, hankalinsa ya kwanta, ya so ya je gidan nata ya tabattar amma har ga Allah ba ya ƙaunar shi, duk da sau ɗaya ya taɓa ganinsa, ranar ɗaurin auren a masallaci, kawai a jikinsa yake jin azabatar da jauhar yake yi, dan ba zata faɗa bane kawai. Al'amin kuwa, su walid suna ta hirar irin tashin hankalin da matarsa ta shiga, da aka kai shi prison, da irin aiken da ta din ga yi masa da kayan amfani yana prison. Gaba daya sai ya tafi lissafin yanzu idan ya saketa, to abinci fa? Amma shi duk da haka gani yake hakan ne mafita, wannan tashin hankalin da take shiga idan ya shiga cakwakiya, sai ya ga kamar yana shiga hakkinta da yawa, kuma a idonta yake ganin damuwa idan ta ganshi a halin maye. Da daddare da ya dawo, yadda ya fita ya bar kayan karin kumallo, haka ya dawo ya tarar da su, ba ta taɓa ba, sai yayi tunanin ko wani abun ta ci, dan haka ya ƙarasa hallake buredin da ƙwan, ya shige ɗakinsa ya cigaba da busa hayaƙi cikin nishaɗi. Washegari ya din ga zaman jira, ya ga ta fito ta yi abun karyawa, amma shiru, gashi bayan sallar asuba ya yi shaye-shaye dan haka yunwa yake ji sosai. Ganin har sha ɗaya ba ta fito ba, ya sanya ya fice, sai dai kuma yajin aiki ake yi, da ƙafarsa ya tafi unguwar su, wurin su Walid. Yau ko tsintsiya jauhar bata ɗauka ba, tana ta fama da kanta, da la'asar ya dawo, ya sake tarar da gidan yadda ya bar shi. Gaba ɗaya sai gidan yayi masa wani iri, ya kwashe kwanukan da ya karya da su jiya, ya fara tunanin ko fushi tayi, shi ne ya sanya taƙi yin shara a gidan. Yana tsaye yana kallon falon, ya ɗaga kai ya ga ta fito daga ɗakinta, kamar fuskarta ta kumbura. Ya tsaya yana kallonta, ya ga tana ɗaga ƙafa da kyar a hankali. Kawai ta yanke jiki ta faɗi a wurin, a sukwane ya yo kanta, ya ɗagata. ta motsa da ƙyar, hannu ya saka ya juyota jikinsa sosai, wani irin hucin zafi jikinta yake fitarwa, ta ɗaga idonta da ƙyar ta kalle shi, idanunta sun yi ja sosai da sosai ta mayar da su ta lumshe. Hankali tashe ya ce "Menene?" "Kaina ne zai fashe" tayi maganar hawaye na bin gefen fuskarta, kafin yayi magana, jikinta ya hau karkarwa, haƙoranta na karo da juna, idonta na neman juyewa saboda zafin zazzaɓi da matsanancin ciwon kai. Ɗagota yayi sosai ya ce "Ki na ji na?" Ta ɗaga masa kai da ƙyar. "Zan je in samo abun hawa, mu je asibiti" "Yajin aiki ake yi, ka manta?" tayi maganar a galabaice. Sai yanzu ya tuna, dan da ƙafa ya je yawonsa ya dawo, ƙungiyar ƙwadago na jagorantar yajin aiki da kuma zanga-zanga domin janyo hankalin gwamnati a kan wasu haƙƙoƙin 'yan ƙasa. "Na sani, yanzu zan dawo" Ba tare da ya san in da zai nufa ba, ya kwantar da ita kawai ya fita, a ransa yake jin idan ya bar yarinyar nan da ciwo, bai yi wa kansa adalci ba. A titin unguwar, ya ga wani ɗan adaidaita sahu, ya tsayar da shi ya ce "Malam mara lafiya zaka ɗaukar mini" Mai baburin ya ce "A'a yi haƙuri ba aiki na fito ba, ba ka san ana yajin aiki ba ne maigida?" "Ana yajin aikin amma ka fito da babur?" "Eh na yi wani uzuri ne, gida zan koma". A ɗan hasale ya ce "Mara lafiya zaka ɗaukar mini" Shi ma a hasale mai baburin ya ce "Na ce ba zani ba, ana dole ne? Ka nemi wani mana" A fusace ya daki tayar gaban adaidaita sahun, mai napep ya waro ido ya ce "Malam meye haka?" Kawai ya shiga bayan adaidaita sahun, ya zare wuƙa ya ce "Bi cikin layin nan, ko na zaro hanjinka yanzun nan da russia" tsit mai ɗan sahun yayi, ya bi layin tare da yin sarandar ƙwace masa baburin ma zai yi. A ƙofar gidan ya saka shi yayi parking, ya sauka ya ƙwace mukullin babur ɗin, ya shiga cikin gidan da shi. Ya ɗauko hijjabinta ya saka mata. "Master" Ya kalleta ba tare da ya amsa ba, ta ce "Yi haƙuri, na saka wahala" "Ki yi mini shiru" Ta ce "To" ya ɗaukkota kamar matacciya, ya shiga da ita napep ɗin. Ya ciro mukullin ya miƙa wa mai baburin ya karɓa yana cunkusa fuska ya ce "Megida amma ka san yajin aiki ake yi, ina zan kai ku? asibitin gwamnati babu aiki". Al'amin ya ce "Ko ma wane asibitin ne mu je" Kamar wata 'yar kyanwa, haka ta kwanta luf a jikinsa, da suka hau kwalta, sai sanyin da take ji ya ƙaru, dan haka ta ƙara shigewa jikinsa, jikinta na ta rawa. Wani Asibitin kuɗi ya kai su a gadon ƙaya, Al'amin ya cilla masa dubu ɗaya, ya rungumi jauhar ya shiga da ita. Ba a taɓa ta ba, sai da ya biya kuɗin file da komai, sannan aka fara yi mata abun da yakamata. suka shiga wurin likita, aka tambayi sunanta, ya manta surname ɗin ta da ya gani a invitation ɗin su, dan haka ya ce a saka mata Zahra Al'amin, shekaru ya ce bai sani ba, sai kintata akayi, aka tura su yin gwaje-gwaje. Bayan sun dawo,ikitan da ya duba ta, yayi ta mita malaria tayi mata mummunan kamu, ga ulcer kuma ga jininta ya hau. Al'amin ya ce "Malam ba lissafi ko masifa zaka yi mini ba, ayi mata abun da yakamata kawai" yanayin yadda yayi maganar, ya sanya likitan gane waye shi. Sai dai Al'amin yayi mamakin jin an ce jininta ya hau. Likitan ya ce "Tana da aure ne?". "Eh" Likitan ya ce "Ayi gwajin ciki, kar mu yi treatment da ka". Al'amin ya ce "Babu ciki" Likitan yayi saroro yana kallonsa. "Malam ni ne mijinta, babu wani ciki, ka yi sauri a fara yi mata abun da yakamata, tana ta murƙususun ciwo. Ko ba ka yadda ba? Al'ada take yi, ko kuna ganin cikin kwana ɗaya ne ko biyu?" Likitan ya ce "Ikon Allah" Jauhar duk da tana fama da kanta, wata irin kunya ta rufeta, ya aka yi ya san tana period ma. Tana ta yinƙurin amai, sai dai babu komai a cikinta, aka ce ya samo mata wani abun ta ci, kafin a fara treatment. Ya fita ya sayo uwar gurasa mai nama, da ruwa ya kawo mata. Ya zo ya tarar, an saka mata ruwa, da allurai. Ya kalli fuskarta, bacci take yi sosai, tana iya ƙoƙarin ta a kan sauro, kar ya cije ta, ba ita ba har shi, da magariba ta yi za ta hau rufe ko ina tana kunna maganin sauro. Abun da bai sani ba, tsananin damuwar da ta shiga bayan kama shi, da maganganun da ya gaya mata jiya ne suka haifar mata da ciwon. Sai dai babbar damuwarsa, hawan jinin da aka ambata. Sai wajejen magariba, ta ɗan samu afuwa. Wajen isha'i aka sallame su, suka yi mata wasu allauran, aka ce masa maza ya kaita gida, alluran suna kashe jiki. Duk kuɗin jikinsa sai da suka ƙare, suna fitowa harabar asibitin, jikinta ya saki ta tafi zata faɗi, ya riƙeta da ƙyar suka fita, sai dai gaba ɗaya titin babu ababen hawa. Ganin sai tangaɗi take yi, kuma bashi da wata dabara ya sanya, ya ɗaure ledar magungunan ta, ya ɗaga ta ya saɓa a bayansa, ya ɗauki takalmanta ya riƙe a hannunsa, ya zagaya ya bi lunguna. A din ga yi ana sauke hakki, idan baki saya ba 0009450228 Aisha Adam jaiz bank Ayshercool 08081012143 30 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci?? Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba?? Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta?? Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki. Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 A ƙalla ya kai awa ɗaya da mintuna talatin, yana tafiya da ƙafa, bayansa ɗauke da jauhar, wani wurin idan da mutane, ayi ta kallonsa, tun da sauran sahun mutane, har ya zama saura ɗai-ɗai. A haka ya isa gida, ya buɗe gidan, ya shiga da ita ɗakinta ya kwantar da ita, zazzaɓin jikinta ya sauka, sai dai gaba ɗaya jikin nata ya saki. Ya kunna fitilar wayarsa yana haskata. Surutai take yi, wanda tun suna hanya take yi, sai dai ba ya gane me take faɗa sai yanzu. "Allah ka shirya mini mijina, Allah ka sa ya daina abun da yake yi. Ya Allah, Allah ka sa ya shiryu. Allah na san ba zaka kunyata ni ba, Allahumma inni as'alukal jannata wa na uzubika mina narr. Rabbana hablana min azwajina, wa zuriyyatuna ƙurattu a'ayunun waja'alna lil muttaƙina imama. Rabbigfir ummi wa abi, warahamhuma, kama rabba ya ni sagira" ta ƙarasa tana shafar fuskarta, da tafukan hannayenta, hakan ya tabattar masa da addu'aoin ta ne na salla, take maimaitawa. Ya lulluɓeta, ya tashi ya sake fita, sai dai abubuwa daban-daban suna ta cigaba da kai komo a zuciyarsa, ya ji ƙwarai yana son sanin wacece yake zaune da ita a matsayin mata, shi dai ya san ba shi da nagartar da uban kirki zai bashi auren 'ya, idan ba da wata a ƙasa ba. Cikin gari ya sake ninkawa ya tafi, bai zarce ko ina ba sai gidansu, ya tarar har sun rufe ƙofa. Bugawa ya fara yi iya ƙarfinsa, Abba ya zo ya buɗe, yana ganin Al'amin ya ruga da gudu ya koma, saboda yana bala'in tsoronsa. Ba tare da ya kula kowa ba, ya shiga kitchen, ya dudduba babu komai sun cinye abincin. Rahila ta fito, ta ce "Kai Aminu lafiya ka zo mana a wannan daren? Yaushe aka sako ka?" "Shahida" ya ƙwala mata kira, kasancewar ya hangota a falo. Cikin hanzari, ta fito ta ce "Gani yaya" Yayi mata alama ta shiga kitchen, ta shiga ya bi bayanta, ya ce "Dafa mini shayi cikin flask ɗin nan" yayi maganar yana nuna mata flask ɗin shayinsu, family size. "Wai Aminu me ka ke yi haka, dan me zaka sakata girki a wannan tsohon daren?" Bai kulata ba, ya kwaso ƙwai ya zube mata ya ce "Ki soya mini wannan ma". Rahila ta koma bedroom ta taso Abbu ta ce "Ta so, ga ɗanka can ya zo a wannan tsohon daren, kar ya yi mana ɓarna". Abbu ya taso ya fito, dan ya fara bacci ma. Ya fito yana faɗin "Kai Al'amin lafiya, ka zo mana a daren nan? Ina matar taka ina gidan naka?". Shahida ta ce "Abbu ka koma ka kwanta, ba wani abu, girki kawai ya ce na yi masa". "Kuma a daren nan, ina matar ta sa?". Abbu yana ta ɓaɓatu, Amma Al'amin bai kula shi ba, sai ma ɗaukko ledar viva, ya buɗe fridge ya kwashe lemon ɓawo ya zuba a ciki, kankana da sauran abubuwan da ya gani a ciki har da su madarar ruwa. "Ka yi masa magana, wannan kayan da yake ɗiba ina zai kai su?". Al'amin ya kalli rahila ya ce "Da kuka aura mini 'yar mutane, ai kun san bani da abun yi, in bari yunwa ta kasheta ko na fara satar kayan mutane ne na kula da ita? Ba ta da lafiya dan haka dole na fito na nemi abun da zan kai mata ta ci". "Da can kai da me ka ke riƙe kanka, ba sai ka nema ba, kuma saboda lalacewa da abun kunya, daga gidanku ne za a ciyar maka da mata? Al'amin ya waiwayo a fusace, ya nunata da yatsa ya ce "Ki kiyayi lokacin da haƙurina zai ƙare a kanki" Shahida ta ce "Yaya gashi na gama, ka ga akwai su maggi ma a nan, tayi maganar tana buɗe drower tana ɗaukkowa. Ta buɗe wata ta ɗebo su taliya da macaroni ta ce "Ka haɗa da su"ya girgiza kai ya ce "Ban da wannan, wannan sun isa" Ta sake cewa "Yaushe zan zo gidanka, ina son kan na koma school na zo muku ziyara, tun da ba ma nan aka yi bikinka, samu zo mu dubata" A taƙaice ya ce "Sai kin zo". Ta ce "Wannan ɗin sun isa, ko kuna buƙatar wani abun?" Ya ce "A'a, sun isa. zo ki rufe muku gidan" ya ƙarasa maganar yana kwasar kayan, ya nufi hanyar ficewa. "Al'amin" Abbu ya kira sunansa, ya tsya cak bai waiwayo ba. "A tunanin auren nan da aka yi maka nutsuwa zaka yi, ka daina wasu abubuwan da ka ke aikatawa, amma abu ya ci tura, ka sanya 'yar mutane a tasku da tashin hankali, meya kai ka ta'amalli da hodar iblis?. Lokaci yayi da yakamata ka daina wasu abubuwan, ko dan kare mutuncinka da na iyalinka. Ko dan ka ga ka sameta a ɓagas ka ke nema ka wahalar da rayuwarta" "Kaga Abbu dan Allah ka daina jan maganar nan, ya tafi kawai su je can su ƙarata, dama ai ba ji take ba ita ma, daidai da ita ne" Wani abu mai nauyi ya haɗiye, ya saka kai ya fice, ba tare da ya sake cewa uffan ba. Bayan ya tafi, Shaida ta ce "Mama dan Allah ki daina tayar da hankalinki a kan yaya, idan yana wannan abubuwan ki zuba masa ido, tun da ba kullum yake zuwa ya yi ba. Abu ɗaya kawai yake buƙata yayi iko da kayan mahaifinsa a matsayin sa na ɗa, kamar yadda muke yi, kin san fa ke da shi, ba kwa jituwa ki din ga kawar da kai a wasu abubuwan da yake yi, yana ɗaga miki ƙafa fa kar yayi miki wata illar". Abbu ajiyar zuciya ya yi, maganganun shahida gaskiya ne, amma shi babban takaicin sa, Al'amin ba ɗan da za a haɗu a rufawa kai asiri bane ba, miyagun halayensa ya sanya ba ya son ya zo ko in da yake. Gaba ɗaya auren da aka yi masa bai sanya ya nutsu ba, kodayeke da sauƙi tun da ya san ya fito ya nemi abun da zai bawa 'yar mutane. Ya koma ɗakinsa, Rahila ta bi bayansa, Amira ta ce "Ohh yau ni nake ganin tsiya, yanzu fa sai a ce ciki ne da ita ko?" Shahida ta ce "Ba abun mamaki bane" "Taɓ, a wannan muzuran da tashin hankalin nass har ta ɗau ciki, iko sai Allah" Al'amin ya sake ninkawa, ya koma gida ya shiga ɗakinta, ya tarar tana ta baccinta, kamar ya tashe ta, sai ya fasa, ya koma ɗakinsa ya kwanta. Bai farka ba, sai wajen tara na safe, a gaggauce ya yi sallar asuba, ya fito falo, ba ta nan ya shiga ɗakinta, tana kwance ta takure wuri ɗaya. "Kin tashi?" Ta jinjina masa kai almar eh. "To taso ki karya ki sha magani" Ta ce "To, bari na yi wanka nayi brush" A hankali ta lallaɓa jikinta, ta shiga ta yi wanka, ta canza kaya ta fito falon. Ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Ina kwana?" "Lafiya ƙalau, bari na kawo miki abinci" Kitchen ya je ya ɗaukko kofi, da shayin da ya zo da shi a flsk, da uban ƙwan da ya saka shahida ta soya masa. Ya ajiye mata a kausashe ya ce "Gashi nan ki karya, ki sha magungunan da suka baki. Saura ki ƙi ci wani ciwon ya kuma kama ki" Ta na fara ci ta ji ta ƙoshi, amai ma take ji. "Wai ba kya so ne ki ke jagwalgwalawa?" Ta ce "Na ƙoshi ne" "A ɗan abun da ki ka ci ne har kin ƙoshi" ya taɓe baki, ya miƙa mata magungunan ta karɓa ta sha. Ya bata wayarsa ya ce "Saka mini lambarki, idan da wani abuk sai ki kira ni fita zan yi" Kallonsa tayi da mamakin yana sane ko wulaƙanci ne, ya sanya yake tambayarta lambar waya. "Bani da waya" ta amsa kanta a ƙasa. Ya mayar da wayarsa aljihunsa ya ce "Shikenan, maganar da nayi miki, ki yi tunani a kai, a ɓangarena ni ina ganin hakan shi ne mafita kawai, amma ki yi tunani abun da ki ka yanke, ki sanar da ni". Dummm ƙirjinta ya buga, kenan haryanzu yana kan bakansa? Ba ta ce masa uffan ba, ya fice. Rasa abun yi tayi, duk da ba ta da tsarki, tayi alwala ta zauna ta kalli gabas, tayi ta addu'a a kan lamarin rayuwarta. Can wurin su Walid ya tafi, in da suke zama su yi shaye-shaye, su naɗa wiwi. Walid ya kalli Al'amin ya ce "Maza lafiya kuwa? Yanayinka ya nuna kamar akwai damuwa". Banza ya yi wa walid, dan haka shi ma ya share shi, ya cigaba da aikin gabansa. Sai kuma can ya ce "Mai laya" "Na kiyayi mai zamani, ya aka yi?" "Dama yara matasa suna hawan jini ne, ba sai tsofaffi ba?" Ya ce "Eh to, na ji an ce akwai wanda ake haifar su da shi ma, amma hawan jini a matasa, maybe damuwa ce ko gado". Ya jinjina kai. Liti ya ce "Maza ko kai hawan jinin ke damu? Kana da 'yar madara, ai ba zaka yi hawan jini ba" Tsuke fuska ya yi, jin liti ya kira jauhar da 'yar madara. Gidansu Al'amin, Abbu ya shirya zai fita ya kalli rahila ya ce "Yakamta idan an janye yajin aikin nan, ku je ku duba matar yaron nan" Rahila ta ce "Taɓ haka kurum, su dai yaran su je ni in je ya illata ni a banza? Su dai su je" Abbu ya ciro kuɗi a aljihunsa ya ce "Amira, ga kuɗi nan ku hau mota, ga dubu biyar ku saya mata fruit ku kai mata, na ji an ce zuwa jibi in Allah ya kaimu, za a janye yajin aikin, sai ku je ku duba jikin nata, kafin na samu na je nima" Ta amsa da to Abbu. Sai dai bayan fitarsa Amira ta ce "Na samu na saka data, dan ba za ta ci 5k ɗin nan ba". Shahida ta ce "Wallahi kuwa da sai na gaya masa, ai ba haka ake yi ba" haka suka cigaba da faɗan su na sakonni. Jikinta ya ɗan yi sauƙi, sai dai ba ta daina ciwon kai ba, ga damuwar abun da Al'amin ya sake nanata mata, kenan yana nan a kan bakansa na rabuwa da ita. Kusan kwanaki biyu, ba ta bari su zauna wuri ɗaya, saboda kar ya sake tayar mata da maganar. Ya gama karyawa, yana kallonta tana ta shirin dutsenta, karyawar ma ba ta yi ba, kamar yayi magana kawai ya shareta, ya tashi ya fita. Su halimatu suka shigo, suka tayata aikace-aikace, sannan suka koma gidansu. Tana falo tana karatunta tana shirin dutse, aka yi sallama a tsakar gida. Ta amsa tare da bayar da izinin a shigo, 'yan mata ne da zasu girme mata su biyu, suka shigo falon. Jauhar ta faɗaɗa fara'arta tayi musu maraba. Suka gaisa da ɗayar, ɗayar kuwa sai hura hanci take yi. Shahida ta ce "Kin gane mu kuwa?" Jauhar ta ce "Na gane wannan ranar da na je gidan, mun haɗu da ita ai, ƙannensa ne ko?" Shahida tayi murmushi ta ce "Kin canka" "Sannunku da zuwa, baku taɓa zuwar mana ko sau ɗaya ba" Shahida ta ce "Ai da yake ba ma zama a gari saboda school, shekaranjiya ya je gida ya ce baki da lafiya, Abbu ya ce lallai mu zo duba ki kafin ya zo shi ma. Ya jikin?" "Jiki Alhamdilillah na warware" "To Allah ya ƙara afuwa, ko mu ce Allah ya raba lafiya, ya kawo mana baby lafiya" Shahida tayi maganar tana murmushi. Buɗe baki Jauhar tayi ta tashi da sauri ta ce "Bari na kawo muku ruwa" Ta kawo musu ruwa, lokacin ta hura gawayi, ta ɗora girki. "Wancan ba tea flask ɗin mu bane?" Amira tayi maganar tana nuna flask ɗin. Jauhar ta ce "Ina ga naku ne, shi ne ya zo da shi, ina ta so nayi masa maganar na waye, yanayin jikina ya hana, amma tun da Allah ya kawo ku shikenan". Suka cigaba da hira da shahida, yayin da Amira ke ta harare-harare itakaɗai. Shahida ta ce "Yaya muka ji da abun da ya faru da yaya na rufe shi da aka yi, Ubangiji Allah ya tsare gaba" Jauhar ta ce "Amin ya Allah, sharri ne ma aka yi masa, amma duk da haka a tayamu da addu'a dan Allah, duk zai daina wataran sai labari. Ina mama?" "Haka ne, ana nan ana yi, mama tana nan ƙalau, tana gaishe ki" Shahida ta sake cewa "Nikam wai dan Allah ya aka yi kuka haɗu da yaya ku ka yi aure, har ya taka ya je gida, sha biyu fa ta wuce, ya ce na yi masa girki matarsa ce ba lafiya na ce wace 'yar baiwa ce haka? Kin san a rayuwarsa ta duniya mata ba sa gabansa mu kanmu yadda ki ka san dodo haka yake a wurinmu". Jauhar za ta yi magana, Amira ta ce "Kin jiki da wata magana shahida, a ina kuwa za su haɗu?, Tallarta fa aka kawo masa ba ta ji, ta fanɗare a gida an rasa yadda za ayi da ita, aka haɗa su, aka jogana masa, da yake shi ma ba sanin ciwon kansa yayi ba, ko ke baki san zancen ba? Kin zauna kina ta zuba ni ina da wurin zuwa" ta ƙarasa maganar tana tashi tsaye ta ɗauki jakarta tayi waje. Gaba ɗaya jauhar ta yi sak, jikinta yayi shock, yayi wani irin sanyi da mamakin maganganun Amira. Cikin dirircewa shahida ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri, wallahi ƙarya take yi, ina zuwa" ta lallaɓa ta ɗauki takalmanta cikin tsananin jin kunya ta bi bayan Amira. Biri yayi kama da mutum, duba da yadda aka yi auren cikin gaggawa ko wata guda ba a rufa ba, ashe abun da aka gaya musu kenan a kanta? A take ta ji ciwon kanta ya tsananta, ta fara tunanin wace irin muguwar ƙiyayya ce tsakaninta da 'yan gidansu har haka. Gidan su jauhar, Hafsa ta shigo daga zance, ta zauna a tsakar gida, Yaya saifu ya shigo, ya kalleta ya ce "Daga ina ki ke?" "Zance" ta bashi amsa kai tsaye. "Wurin wa?" Tayi shiru tana kallonsa. Ya ce "Wallahi kun yi asara, yanzu dama Saboda hafsa ta auri mutumin nan, da yake son jauhar shiyasa ku ka aurar da ita ga mutumin banza, wallahi ba ku kyautawa kanku ba, kuma da ikon Allah sai Allah ya saka mata". Mama ta ce "Saifu maganar me ka ke yi ne ban fahimta ba?" Ji yayi kamar ya gayawa mama baƙar magana, sa'arta ɗaya mahaifiyarsa ce, babu yadda zai yi da ita, kawai ya fice. Mama ta ce "Zakiyya, da gaske mutumin nan ne yake zuwa wurin Hafsa?" Ta haɗa rai ta ce "Ni ma ban san zancen ba sai yanzu" Mama ta ce "To meye abun ɓoyewa ban da abunki, ai abun farinciki ne a gare mu baki ɗaya. Dama ai jauhar ɗin ce ba ma son ya aura, wallahi nayi murna haƙanmu t cimma ruwa". Sai kuma ta ɗan saki ranta ta ce "Wallahi ina ta son na gaya miki, abubuwa ne sun sha mini kai, kuma ba gama daidaitawa suka yi ba" "Ai bakomai, Allah ya tabattar mana da alkhairi" suka gama maganar ta shiga ɗakinta, ta jinjina kai ta ce "Hmm zakiyya kenan, baki da wayo da ni ki ke zancen, duk wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi, zaki gane kuskurenki". Yau tun la'asar ya dawo, kwana biyu ba ya yin dare, saboda rashin lafiyarta sai dai fa ba zai ce mata sannu ba. Ya kasa gane kan yanayinta, ta zuba masa abinci, ta koma gefe ta yi shiru. Ya gama ya tashi ya tafi ɗaki, zai ɗan kwanta ya huta, kasa jurewa ta yi ta tashi ta bi bayansa. Ta ssme shi, yana ta watso kayan wardrobe ɗin sa da ta gyara da ƙyar. "Master" "Yeah" ya amsa ba tare da ya kalleta ba. "Ƙanneka sun zo ɗazu baka nan" "Ok" kawai ya ce, amma ƙasan zuciyarsa mamaki yake yi, tun da ƙannensa ta ce, da ƙanwa ta ce ya san shahida ce kawai. "Dan Allah abu nake son tambayarka, na san kai ba ma'abocin ƙarya bane ba, na san ba zaka fara a wannan karon ba" bai amsa ba, dama ba tayi tsammanin hakan ba, ta ce "Da gaske tallata aka kawo maka, wai ba na ji na fanɗarewa iyayena shi ne aka aura maka ni?" Ya ɗaga rigar hannunsa yana kallo kamar ba zai yi magana ba sai kuma ya ce "Eh, haka na ji" Cikin rauni ta ce "Kuma ka yarda?" "Kusan haka, dan na san ba yadda za ayi a aureni haka kurum babu dalili, a abun da bai wuce sati biyu ba" Yayi maganar yana ajiye rigar, ya ɗauki wata, sautin da tayi na ƙwacewar kuka ne, ya sanya shi ɗagowa a tsorace yana kallonta. Cikin kuka ta ce "Wallahi ni ba lalatacciya ba ce, ban fanɗarewa iyayena ba, dama kallon da ka ke yi mini kenan, kallon da 'yan uwanka da sauran mutane suke yi mini kenan" da ƙyar maganarta take fita, saboda numfashinta da ya fara sama. Ya ƙaraso gabanta ya ce "Wai ke ba kya gajiya da kuka ne? Komai kuka?" Hannunta take fifitawa kusa da hancinta, alamar numfashi yana bata wahala, da sauri ya ɗauketa ya fita da ita tsakar gida, ta lumshe idonta hawaye na bin gefen fuskarta, sai dai ƙirjinta sai ɗagawa yake yi yana sauka, alamar numfashin da ƙyar take yi. "Ko mu koma asibiti? dama sati ɗaya suka bamu mu koma" Ta girgiza masa kai. "Ba zaki daina kukan ba?" Maimakon ta daina, sai ma wata sheshsheƙa da ta zo mata, ga numfashinta yayi nauyi. Ya ciro wayarsa a aljihun wandonsa, ya kira liti. "Maza ya ne?" Viper ya ce "Kana ina?". "Na shiga area raba kaya". "Samo adaidaita sahu, ka zo gidana zan mayar da 'yar madara asibiti" "An gama mazaje" Zai ajiye wayar, ta fara vibrating, ya ɗaga bai yi magana ba. "Honorable ya dawo, akwai taron gaggawa da zai yi, yana son ganinka" "Na ji" "Dan Allah kar ka ɓata lokaci sosai, ka san zaɓe yana ƙara gabatowa" Ras jauhar ta gane muryar waye, muryar P.A ce, a take ta jinjina rashin kunya irin na ɗan siyasa. "Dan Allah kar ka je, idan ka tafi mutuwa zan yi" "Allah ya jiƙanki" A sanyaye ta ce "Amin, amma dan Allah ko na mutu kar ka je ba na son ka din ga zuwa wurin 'yan siyasa" "Ki yi mini shiru, idan ba haka ba zan tashi na bar ki" "Yi haƙuri" ta faɗa tana haki. A hankali take iya takawa, saboda numfashinta, ya sakata a napep ɗin da liti ya zo da ita, sannan ya shiga, liti ya zauna a gefe suka tafi Asibiti. File ɗin ta aka kai wa likita, shi da ita suka shiga, liti kuma yana can waje. Likita ya ce "Ka ƙi yadda ayi mata gwajin ciki, gashi tana ta fama da an duba dai" Ya ce "To duba" Jauhar ta ce "Ni bani da komai". "Shikenan, ki na da athma ne dama, wannan hakin da ki ke yi?" Ta jinjina masa kai ta ce "A'a allergy ne, shi ma kuma tun ina yarinya ne" Al'amin ya kalleta, likitan ya sake cewa "Akwai magani da ki ke sha ne? Ai kusan duk abu ɗaya ne, allergy ɗin da athma" Ta girgiza kai ta ce "A'a ai na daɗe ba na shan magani, addu'a nayi ta yi, ya  daina tashi, tun ina ƙarama sosai ban kum jin alamun sa ba" Likitan yayi murmushi ya ce "Masha Allah, ka ga 'yar baiwa, to a din ga sakamu a addu'ar mu ma, amma dai yanzu zan rubuta miki magani, sai ki kiyayi hayaƙi, ko kin shaƙi wani abun ne?" Ta ce "A'a kuka na yi kawai na ji na kasa numfashi sosai" Likitan ya jinjina kai, ya ce "Bari na duba bp naki na gani". Shi dai gogan bai ce komai ba, likitan ya duba bp ɗin ta sannan ya ce "Zahra kina shan magungunan da na baki kuwa?" "Ta jinjina kai alamar eh". "A iyayenki akwai mai hawan jini?" Ta ce "A'a" Ya kalli Al'amin ya kalli jauhar ya ce "Akwai abun da yake damunki ko?" Tayi yaƙe ta girgiza kai. "Zahra, ita rayuwar duniya haƙuri ake yi. Malam ka zauna da matarka ku tattauna idan a cikin aurenku matsalar take, a magance ta, idan ba haka ba, hawan jinin nan zai iya taɓa mata zuciya, idan wani abu ka ke yi mata da ba ta jin daɗin sa, ku tattauna dan Allah ku fahimci juna, amma tayi ƙanƙanta da wannan ciwon" "Zahra" likita ya kuma kiran sunanta, kamar yadda ya gani a jikin file. "Idan kun je gida, ki zauna da mijinki, idan damuwa ce da ke, ki gaya masa, ki cire koma menene a ranki, mijinki da kuma al'umma baki ɗaya muna buƙatar ki a raye" kawai ta sunkuyar da kai sai kuka. Al'amin ya ce "Rubuta mana magungunan kawai mu tafi" Ya rubuta maganin, ya bawa Al'amin yana kallon jauhar cikin tausayawa. Al'amin ya kalleta ya ce "Mu tafi? Ko yau ma goyakin zan yi?" A hankali ta tashi tsaye, ya ce "Kin daina hakin?" Ta ce "Ya ragu" Ya saka hannunsa ya riƙe nata, suna tafe a hankali har suka fito wajen asibitin in da pharmacy yake, ya saya mata maganin suka hau napep ɗin da ya kawo su zuwa gida. Shi dai bai iya rarrashi ba, bai ma san ta ina zai fara ba, amma gaba ɗaya yanayin da jauhar take ciki, bai yi masa daɗi ba, ya san fiye da rabin damuwar ta shi ne sila, ya ce su rabu kuma ta cigaba da kuka. Tana kwance a kan kujera, tayi lamo, shi kuma yana zaune a ƙasa, yana kaɗa ƙafa. "Master" "Mmm" "Kana ta ɗawainiyar asibiti da ni, na gode sosai Allah ya saka da alkhairi, ya ƙara arziki" "Amin" Ta sake cewa "Master" Ya ɗago yana kallonta. "Dan Allah da gaske kallon mara ji wadda ta fanɗarewa iyayenta ka ke yi mini?" "Haka aka ce mini ai" Ta ce "Aishikenan, shiyasa ka ke so ka sake ni?". Ya ce "A'a kina takura mini ne kawai, kin isheni yanzu ina zaman zamana ba zan fita ba, sai dai na zauna kula da ke" Ta ce "To ka yi haƙuri, dan Allah kar ka fita yanzu, ji nake kamar kana fita zan mutu" idan tayi zancen mutuwar nan, gabansa faɗuwa yake yi, amma ya maze ya ce "To zan hanaki mutuwa ne?". "A'a, amma dan Allah ka daina yi mini kallon mutuniyar banza, dan Allah ka gaya wa 'yan gidanku, aje ayi bincike ma a kaina, wallahi ba mutuniyar banza ce ni ba" ɗago ido yayi yana kallonta, kenan zuwansu ne suka gaya mata wannan maganar, yayi shiru ya cigaba da latsa wayarsa. "Master" " 'yar madara" ya amsa bai kalleta ba. Likita ya ce "Ka daina yi mini abun da na so, ka tambaye ni abun da nake so ka daina yi mini" Ya ce "Tom" ɗan murmushi ta yi, yau tayi sa'a ana amsa mata ma. "Yaushe zaka sake nin?" Ya yinƙura ya tashi ya ce "Na fasa yanzu, sai an kwana biyu, idan aka yi yanzu ina ga warewa zaki yi". Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, ya shiga ɗakinsa. Cikin ikon Allah, washegari ta tashi jikinta da sauƙi, sai dai damuwar cewar ita fanɗararriya ce, ta kasa barinta. A tsakar gida ya taso, ya tarar da ita, tana aiki. "Ina kwana" "Kin warke ne?" Ta girgiza kai ta ce "A'a, bayan ba ka zauna mun yi maganar da likita ya ce ba" "Akwai abinci ne?" Ta ce "Eh shinkafa na dafa amma akwai sauran buredi in dafa tea" Ya ce "Zubo mini, ke ki sha tea ɗin" Ta zubo abincin ta kawo masa, ya kalleta fuskarta duk ta faɗa. "Amma yau ba zaka fita ba ko? Ka zauna ka kula da ni" Murmushi ya yi da gefen bakinsa, ta sake cewa "Idan ka gama cin abincin zan gaya maka abubuwan da nake son ka daina yi mini, ko sannu baka yi mini bama". Tayi ta zuba, amma yayi gum. Wayarsa da take ringing ya ɗaga ya ce "Ina sane zan zo yanzu" Ta haɗe rai ta ce "Amma ba fita zaka yi ba ko?" Ya ce "Fita zan yi" "Ni dan Allah ka zauna ka kula da ni" shagwaɓa da rikici kawai take yi masa tsakanin jiya da yau, kamar yau an cire mata tsoron sa. Ta tashi ta ɗauki kwanukanta, ta tafi kitchen cike da takaici. Ko ba zai kulata ba, tana son ganinsa a gida. Sosai ta ji ranta ya yi mugun ɓaci fitar da zai yi, ɗan tattalin da aka yi mata jiya zuwa yau yayi mata daɗi, duk da ana yi ana haɗe mata rai. Tana cikin ƙunƙuni, ya fito da sauri hannunsa da wayarsa a kunnensa, hannunsa ɗaya da makamin da yake kira da iraƙi. Ya ce "Gani nan, ka duba bayan nan, russiata da sweazland suna nan, ka ɗaukar mini su, kar ku bari su motsa, gani nan zuwa" hannunsa ɗaya yana soke makaminsa iraƙi a cikin ƙugunsa. Ya ce "Fitar gaggawa ta kama ni, idan nayi dare ban dawo ba, ki rufe ƙofa, duk wanda ya buga kar ki buɗe, idan na dawo na hauro" Banza tayi masa, ta cigaba da yanka albasarta. "Ke ba magana nake yi miki ba?" Shiru ta sake yi masa. Ƙoƙarin leƙawa yake yi, ya ga ko lafiya. Kawai ya ga ta jefo masa murfin tukunya, a zatonsa ko ba ta san me tayi ba, kawai ya ga ta sake jefo masa rariya. Saroro ya tsaya cikin mamaki, ta cigaba da zaro kwanuka tana jefa masa tana kuka, bai ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da suka haɗa ido ta jefo masa ludayin hannunta a ƙirji. Ayshercool 08081012143 31 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Tunani ya fara yi, ko tana da aljanu ne. Ganin idan ya ƙyaleta, fashe-fashe za ta yi, ya sanya shi takawa ya riƙo hannunta, amma sai ƙoƙarin fizgewa take yi. Kasancewar ba ta yi masa wahalar ɗauka, ya sanya ya danƙota kamar kazar cikin akurki, aikuwa ta cigaba da fizge-fizge da ƙoƙarin ƙwacewa, falo ya shiga da ita, ya tattara hannayenta ya riƙe, hakan ya sanya ta kasa cigaba da ƙoƙarin ƙwacewar. "Meye haka ki ke yi? Kanki ɗaya kuwa?" Kallonta yake yi, har ta fara kuka, shi bai ma san me yayi mata ta aikata hakan ba. "Me nayi miki ki ke jifana?" Cikin takaici ta kalleshi ta ce "Meye ma baka yi mini ba, ni bani da wani amfani a wurinka, bani da ikon roƙon alfarmarka, komai ma yi mini ka ke yi, ko yayi mini daɗi ko akasin haka, ba ka tausaya mini dama ka tsane ni, so kake yi na mutu ka huta". "To yanzu kuma me nayi miki?" "Wuƙa fa ka ɗauka zaka fita, idan aka yi maka wani abun ko ka yi wani laifin nikaɗai nake fama, sai su yaya walid da suke taimaka mini, amma kai gaba ɗaya baka tausayina, ba ka tausayin maraicina saboda da ma ba so na ka ke yi ba. Kodayeke ba laifinka bane, tun da sama ta ka aka aura maka ni, bayan an gama ɓata ni a wurinka. Ko hira ba ka yi da ni, in tayi maka magana kayi mini shiru, idan aka ga na mutu kai ne, sai ma na rubuta na bar wasiyya, idan na mutu kai ka ƙarasa ni da takaici" Yayi shiru ta din ga yi, tana faɗa tana kuka, sai da ta gama tsaf, sannan ya miƙe ya ce "Ki kula da abun da na gaya miki, kar ki fita kar ki bar gida a buɗe, idan na yi dare ki kwanta zan hauro". Ta ɗaga idanunta da suka yi ja ta ce "Sai ka fita ko?" "Ai na ce idan ba zaki iya ba, ki koma gidanku ko ban gaya miki ba?" Tayi shiru ranta na yi mata wani irin zafi, ya fita ya kwashe kwanukan da ta watso waje ya fice. Unguwar su ya nufa, faɗa ya haɗa ɗan unguwarsu, da ɗan unguwar su madaki, yaron ya kwaso 'yan daba yaran madaki, sun shiga unguwar su Al'amin su na ta faɗace-faɗace. Yana zuwa chamber su, ya ɗaukko wuƙaƙensa, ya fita, sai dai da ya je, yaran suka din ga darewa, saboda wanda suka taɓa karo da shi, sun san irin ƙarfin da Allah ya yi masa. Wani yaron madaki ne, da yake ji da tashen balaga da rashin mutunci, ya sha gaban Al'amin yayi yana zage-zage yana ƙoƙarin saran Al'amin. Ya jefar da wuƙarsa, ya nufi yaron, wanda suka san Al'amin suka din ga ce masa ya gudu, kar ya bari ya kama shi, amma kasancewar ya yi wa wiwinsa haɗin kauri da wata ƙwaya da suke yi wa laƙabi da 'yar fara, ya sanya yake jin kansa a sama, ko barikin sojoji zai iya shiga yayi rashin mutunci. Duk iya ƙoƙarin sa ya kasa saran Al'amin, saboda yadda yake da zafin nama, wurin kare saran, wanda idan ba professional athlete ne ba, babu lallai ya iya. Ya shammaci yaron, ya soka masa iraƙi a cinyarsa, a take ya kurma wani uban ihu, liti ne ya karyo kwanar, riƙe da nasa makamin yana ɗigar da jini, "Mai zamani yi haƙuri, kar ka karya yaron nan" sai dai bai rufe bakinsa ba, ya ga Al'amin ya fito da dogon harshensa, ya lashi laɓɓansa na ƙasa da su, idan har yayi haka sai aiwatar da muguntar da yayi niyya, kan liti yayi wani yinƙuri ya karya ƙafar yaron ya watsar da shi yana kururuwa. "Mai zamani, yanzu zaka sake janyo mana faɗa, madaki zai ce sai ya ɗauki fansa, da baka karya shi ba" Ya ɗago jajayen idanunsa a slow, yayi wa liti wani irin kallo ya ce "Ya zo ya ɗauki fansar a kaina, idan ya isa" ya wulwula iraƙinsa, ya cafe ya yi gaba. Kai tsaye gidan su ya tafi, da wannan wuƙar tana ɗigar da jinin da ya soki yaron nan. Yana shiga ya wuce falo, sai ganinsa suka yi a tsaye a kansu da makami tsirarsa. Salati suka fara yi da kururuwa, ya kalle su ɗaya bayan ɗaya, "Me ya kai ku gidana?" Yayi maganar yana kallon shahida. Cikin tashin hankali ta ce "Abbu ne ya ce Mu je mu duba matarka". "Shi ya ce ku je ku gaya mata cewar kangarewa ce ta sanya aka yi aurena da ita? Ku je ku ci zarafinta?" Cikin tashin hankali shahida ta ce "Ba ni na faɗa ba Amira ce wallahi". Rahila kuwa hankalinta ya dugunzuma, ta ce "Ka yi wa Allah da ma'aikinsa ka yi haƙuri, dan Allah kar ka yi musu wani abu" Ai kamar ta tunzura shi, ya saka wuƙa a wuyan Amira, "Ya zama na farko ya zama na ƙarshe, ayi duk cin kashin da za ayi a kaina, ban da 'yar mutane da ki ka haɗa kai ku ka cutar, idan aka kuma zan yi ɓarna, wallahi sai na saka wa mutum ƙarfe" Shahida ce ta iya cewa "In sha Allah ba za a sake ba" yayi ƙwafa ya fita. "Amira kin ga abun da ki ka ja mana ko? Da ya illatamu, da kin cuce mu" Amira kam kasa magana tayi, sai dafe ƙirji tana hakin tsoro. Al'amin wuni yayi ranar, yana partrol da yaransa a unguwar, saboda kar yaran madaki su zo su afkawa wanda bai ji ba bai gani ba. Cikin ikon Allah, har dare yaran madakin ba su sake shiga unguwar su Al'amin ba, duk da sun yi artabu sosai da wasu, dan sai da aka yi masa rauni a cikinsa, ya kama hanyar tafiya gida. Jauhar na falo tana karatun exam, duk da sun kusa kammala jarrabawa. Ta katangar ya diro kamar ɓarawo,s an samu cigaba, yanzu idan ya ga dama ya kan yi salama. Sallamarsa kawai ta amsa, ba ta sake kula shi ba, ya wuce ɗakinsa, mintuna goma amma ba ta biyo shi ba, ya fito ya ce "A kawo mini ruwan zafi zan yi wanka" Ta tashi ba ta ce komai ba, ta ɗaukki flask, aurensa da ita ta saba masa da wanka da ruwan ɗumi, saɓanin da da har a kuddudufi wankansa yake yi ya ƙara gaba. Yanzu kuwa kusan kullum, da an kawo wuta, take dafa ruwan a heater, ta saka a flask. Ta zo ta haɗa masa ruwan, sai dai ta ga kamar yana ɓoye wani abu. Kawai ta leƙa ta ga me yake ɓoyewa, yanka ne a gefen cikinsa, ya saka rigarsa yana ƙara goge jinin kasancewar ba mai zurfi bane ba. "Ka gani ko? Sai da ka je aka yanko ka ko? Abun da nake ta gudu, sai da ka zubar da jini ko, ba za kai daina zuwa wurin da za a cutar da kai ba ko master? Kodayake ma ni abun yake damu, kai ko a jikinka". "Na ce ya dame ki ne? Ba jikina bane?" Idan ba gizo idonsa yayi masa ba, hararsa ta yi ta fice. Shi mamaki ma take bashi, tun da ta yi rashin lafiyar nan, take rigima kuma kamar ta rage tsoron sa. Ya shiga ya yi wanka, ya fito ya tarar da ita da ɗan ƙaramin kwanon abinci, sai kuma kayan dressing, tun na lokacin da aka yi masa wancan raunin. Bai kulata ba, ya ja kwanon abincinsa ya cinye, awara ce da miya, ya sha ruwa. Ita ma ba ta kula shin ba, ta saka auduga da spirit tana goge, kan ciwon, tana gogewa tsigar jikinta na tashi, kamar jikinta take gogewa, shi kuwa kamar dutse latsa wayarsa ma yake yi. Haushi ya isheta, ta kalleshi ta ce "Wai ba zafi ne?" "Eh babu, idan ma dirzawa ki ke da ƙarfi, dan na ji zafi, ba na ji" ta tashi ta fice fuuu, tana yi masa fatan shiriya a ranta. Kusan awa ɗaya da rabi, ya shigo mata ɗaki, ta yi sauri ta tashi zaune, saboda ta san tsiyar da ta aikata masa. Ya kunna fitila ya hau yi mata bincike a ɗaki. "Me ka ke nema?" Ya tashi ya nufo ta, ya miƙa mata hannu ya ce "Bani kayana da ki ka sace mini yanzu" "Ni ba na sata" Ya ce "To baki nayi ki ka ɗauka? Ko kema kin fara sha ne ban sani ba? Kodayeke biri yayi kama da mutum, da ki ka iya kallona ki ka din ga jifana nan gaba ina ga swizaland zaki saka mini ina ga" "Ni ba na shan komai, kuma ban ɗau komai ba". "Ba ki ɗauka ba ya aka yi ki ka san a kan me nake magana?" Tayi shiru ba ta ce komai ba. Hankaɗata yayi, ya janyo ledar kayan shaye-shayen sa a cikin bargonta. "Na gaya miki idan kin gaji ba zaki iya zama ba, ban ɗaure ki ba, ki ƙara gaba" A ƙule ta ce "Ka ɗaure ni mana, zan tafi ba ka sallame ni bane, ka rubuta ka gani idan ban tafi ba. Tun da baka da tausayi idan ba mutuwa na yi ba hankalinka ba zai kwanta ba" tayi maganar tana sheshsheƙar kuka. Ya kalleta, gaba ɗaya ko faɗan ba ta iya ba, voice ɗin ta sam ba na masu faɗa bane, shagwaɓa kawai take yi. Ya ce "Kin yanke hukunci kenan? Ai da kin gaya mini da duk ba a zo nan ba, zan rubuta na baki, dama na gaji". "Kuma wallahi idan ka yi shaye-shaye kai da Allah" Bai kulata ba, ya jefo mata kwalin sabuwar waya gal, ya ce "Gashi nan, akwai layi a ciki na yi rijista, idan kuma na yi wani laifin na gudu ke za a kama". "Bana so" ta faɗa tana kwanciya, duk da ƙasan zuciyarta tayi mamakin wayar. Ya saka hannu ya ɗauka ya ce "To kin huta" ya fice ya bar ɗakin. Ta kwanta ta yi shiru, sai ta fara tunanin ya aka yi ya ɗaga mata ƙafa ya ƙyaleta, sai kuma ta ga rashin kyautuwar abubuwan da ta yi masa. Bayan sallar asuba bacci ta koma, ƙarfe takwas da rabi ta farka, tana ƙoƙarin saukkowa daga kan gadon, tayi tozali da farar takarda da biro. Gabanta ya faɗi ta ce "Na shiga uku sakin nawa ya yi?" Ba ta taɓa takardar ba, ta saukko a sukwane ta tafi ɗakinsa sai dai baya nan ya fice. Gaba daya jikinta yayi sanyi, sai yanzu ta ƙara jinjina girman wauta da aikata. Yau rahila har gidan su jauhar ta je, suka ƙule a ɗaka ita da Anty Zakiyya suna ta surutu da shewa. "Zakiyya ina ga 'yar ku fa an gamu laulayi take yi" "Kai haba dan Allah" "Wallahi da gaske, ke 'ya mace shu'uma komai ƙanƙantarta, kin san yaron nan har gida ya zo da wuƙa ya gama ta'addancin sa tana zubar da jini, zai yi mini hauka a gida wai su Amira sun je masa gida sun yi matarsa ko me oho musu, na ga tashin hankali na ce iyee yanzu har ta samu wannan matsayin. Wallahi mamaki nake yadda ta iya zama da yaron nan" Zakiyya ta ce "Ba ki ganta ba kamar sokuwa, kafin ki ga ta yi fushi, ko tayi zuciya da abu za a jima, ko kuma kawai tsabar ƙarfin hali ne da ƙi faɗi ba" Rahila ta ce "Sai ta yiwu, ya ake ciki da maganar hafsa?" "Mu na nan ana ta murginawa, ana shirin kawo kuɗin aure, na ce lallai ta ce masa a haɗo da kayan lefe, ana sallacewa ayi auren, duk da wannan matar ta nuna bakomai na san tsohuwar muguwa ce, wataƙila wani abun zata kitsa, dan haka kan tayi wani yinƙuri ayi a wuce wurin". "Yauwwa kar ki kuskura ki sakankance ko ki yadda da ita, ni ban zaci lamarin ma zai zo da sauƙi haka ba, ku cigaba da tatsarsa kuna tarin kayan aure" Zakiyya ta ce "Ke kin ga hidima, ai ni dai Allah ya kashe ya bani, da yanzu sai dai mu ga ana yi wa waccan yarinyar jauhar" Rahila ta kwashe da dariya ta ce "Ga mijinta can suna fama, amma wallahi ya fara son yarinyar nan, kai amma ba ƙaramin haƙuri take yi ba bala'i Allah ya kyauta" suka cigaba da hirarrakinsu, da shirin biki. Misalin ƙarfe ɗaya da rabi na dare, suka fito daga taron meeting, daga ofishin jam'iyya, sakamakon gabatowar manyan zaɓuka da za a gudanar a cikin Nigeria. Yau bai san iya adadin meetings ɗin da ya yi attending ba, suka jero da shi da mataimakin firaministan jam'iyya na jiha, ya ɗan yi miƙa ya ce "Kai, yau na gaji over" "Kai honorable, da an yi babban zaɓe an wuce wurin, haka ne, ka san ban yi sati da shigowa daga Abuja ba, can ma wasu tarurrukan ne, abun duk babu sauƙi, ina ta ƙoƙari in sha Allah sai na kawowa excellency yankina, ina nan a satin nan zan yi empowerment na matasa, kuɗina duk sun tafi a campaign ɗin nan" "Kar ka damu honorable, hannun jari ka saya, da an wuce wurin sama zaka din ga kwashe ribarka, ka mayar da uwar da ribar ka ɓace ba zasu sake ganinka ba, sai bayan shekara huɗu" suka kwashe da dariya. Suka yi sallama, kowa ya nufi motarsa, ko da ya je gida, matarsa tuni tayi bacci, yayi wanka ya nemi wuri ya kwanta, dama ba yunwa yake ji ba, sai dai bacci ya gagare shi, ya din ga juyi a kan gadon, ga gajiya ga baccin yana ji, amma ya kasa ya ɓuge da lissafe-lissafe abubuwan da yake son yi idan ya dace ya samu ya ci zaɓen nan. Ji yayi kamar kansa zai fashe, saboda stress kawai ya tashi ya ɗauki mukulli, ko direba bai nema ba ya hau motarsa ya fice. Yamma da gari yayi, ya hau kan titin gwarzo road kasancewar dare ne, titin babu ababen hawa, ya sauke glas ɗin motar kaɗan, yana tafe a hankali yana shaƙa wani abu a hancinsa. Sai d yayi nesa da cikin gari sosai, sannan ya yi parking a gefen hanya, ya rufe glasan motar, ya cigaba da shaƙa abun nan, kusan mintuna talatin, sannan ya juyo kan motar ya nufi dawowa yana tafe iskar kan titin nan na ratsowa cikin motar, sannu a hankali har ya koma gida. Jauhar kuwa tun da tayi tozali da takardar nan ta kasa nutsuwa, ta kasa zaune ta kasa tsaye, kuma taƙi buɗe takardar, da ta leƙa ta hangota ma, sai ta yi sauri ta fito daga ɗakin, ta din ga lissafa irin halin da za ta shiga idan ta koma gida, da irin dariyar da za su yi mata. Kuma yaƙi dawowa, har dare ba ta ganshi ba, hakan ya ƙara sanyata cikin tashin hankali, ba irin tunanin da ba ta yi ba, har ta fara tunanin ko da ya saketa, barin gidan yayi gaba ɗaya, sai dai kayansa suna nan, dan ita ta gyara ɗakin ya watso da komai ya bar mata a wurin. Sai sha biyu saura ya dawo, idonta biyu ya dawo ba ta yi bacci ba, sai da ta tabattar ya shiga ɗakinsa, sannan ta ɗauki takardar ta bishi ɗakinsa. Yana kwance a kan katifarsa, ya cika ɗakin da warin taba. Yanayinsa ya nuna a buge yake, saboda fitilar ɗakinsa a kunne take, ya haye katifa ya mimmiƙe idanunsa sun yi ƙanana da ƙyar yake ɗaga su, kallo ɗaya ya yi mata ya mayar da idonsa ya lumshe. "Master sai da ka rubuta takardar nan hankalinka ya kwanta ko?" Bai buɗe idonsa ba ya ce "Ke ki ka ce na rubuta" "Kuma sai ka rubuta ɗin ko? Saboda ina fargabar kar ka sake ni, bakomai maraici ne ya janyo mini, Allah ya gani na yi iya yi na, na yi biyayyar aure, amma kullum kallona ka ke yi wadda ta takura rayuwarka, ga takardarka nan, ban ma buɗe ba balle na san meye a ciki, kuma wallahi ban saku ba" ta dire masa takardar a jikinsa, ya ziro harshensa tare da naɗe shi ya mayar, ya gyara kwanciyar sa, har ta gama surutanta, bai kuma motsawa ba. Kasa bacci tayi, ta ɗaura alwala ta tayar da salla, ta din ga addu'a Allah ya sa ya fasa sakinta, saboda ita a ganinta gara ƙalubalen gidan Al'amin a kan na gidansu. Duk rintsi ba zai daketa ko ya ci mutuncin ta ba, ko yi mata sharri ba, sai dai miskilancinsa da gaya mata baƙar magana wasu lokutan da har daɗi take ji ya kulata, ciyar da su kuma da take yi mafi yawan lokuta baya damunta, sai ma yi wa Allah godiya da take yi da ko yaya ba ya hanata abun da zata sarrafa su ci, ko yaya ta kasa abun sayarwa za a saya dan ma ana yi mata mugunta. Bayan sallar asuba tayi shiru tana tunani, ta ga sam ba ta kyauta ba, wasu abubuwan da ta yi masa, tun daga jifansa da kwanuka, har zuwa tsiwar da ta yi masa, ita tayi mamaki ma da ya ƙyaleta. Yau ba ta iya komawa bacci ba, ta fito aikace-aikacen ta, tana yi tana leƙawa ko ta gani ko ya tashi. Tana falo ta jiyo motsinsa, ta tashi ta shiga ɗakin da sallama. Ya amsa mata, ba tare da ya kalleta ba. Jiki a sanyaye ta durƙusa ta ce "Master ina kwana?" "Lafiya ƙalau" "Ka tashi lafiya, ya ciwonka?" Sai a wannan karon ya kalleta sai dai bai ce komai ba. "Master dan Allah dan Annabi ka yi haƙuri ka yafe mini, abubuwan da na yi maka kwanan nan ban kyauta ba, dan Allah ka yi haƙuri ba zan sake ba, wallahi ni ba mara kunya ba ce, kawai na rasa ya zan yi da wasu abubuwan ne, damuwa tayi mini yawa, dan Allah ka yi haƙuri idan ka sakenin ma, ka yi haƙuri ka mayar da ni" tayi maganar cikin rauni. Ya lumshe idanunsa ya ce "Bani wuri zan kunna hayaƙi" Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri master, ka yafe wa 'yar madara ɓacin rai ne ba zan sake ba, na san ban kyauta ba, dan Allah ka yi haƙuri" "Sai fa kin tafi, kin isheni ne kawai takura mini ki ke yi" "Dan Allah ka yi haƙuri, na daina takura maka, har cincin na yi maka jiya, in kawo maka?" "Eh ki kawo mini, sai fa kintafi" "Da ka san abun da hakan ka iya haifar wa rayuwata, da baka sake ni ba, dan ka ga ina ta roƙonka shikenan, duk ranar da ka bari na bar rayuwarka na bar ta har abada lokacin da zaka so ka ganni da kuɗi ba zaka ganni ba". "Eh na ji, kafin ki fara ɗaukar makami, gara mu rabu, ungo takardarki tafi da ita" yayi maganar yana danƙa mata takardar da ya warware. Ta rintse idanunta, tuni ta fara kuka, ta buɗe idanunta ta sauke a kan kyakkyawan rubutunsa, dan ganin saki nawa ya yi mata. *Ba zan dawo da wuri ba, na bar kuɗi a kan katifata ki sai wani abun ki ci* Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, ta ce "Shi ne ka yi ta wahalar da ni? Dama ba sakina ka yi ba, ka sakani kuka?" Hamma yayi, yayi shiru ta ce "A'uzibillah" duk gurbin da ya yi wani abu, yakamata ya yi addu'a bai yi ba, sai tayi masa. Ta ce "Aishikenan amma dan Allah ka yi haƙuri abubuwan da na yi maka ka yafe mini" "To, ki bani wuri zan sha abu" Ta ce "To bani wayar da ka bani jiya" gefen katifarsa ya nuna mata, ta tashi ta ɗaukkota a kwali. Ta kalleshi ta ce "Yanzu dan Allah wannan ta wa ce master? To kai ina taka?" Ya nuna mata keypad ɗin sa. "Wallahi ko a mafarki ban taɓa tunanin riƙe waya ba, yaya saifu ya taɓa bani keypad mama ta ƙwace, Allah ya saka maka da alkhairi ya saka ka a aljanna, Allah ya nuna mini ranar da zaka daina shan komai, ka zama limami saboda salihancinka, Na gode master na gode sosai da sosai" tayi maganar tana tattaɓa wayar. "To excuse me, ina son yin caji" "To yi mana" Ya ce "Ki fita ki bani wuri dai, kar ki sume mini yau bani da kuɗin zuwa asibiti" Maƙale kafaɗa tayi, ta ce "Master, wai yaushe zaka kai ni na gaida mama ne? Da wurin hajiya ma?". "Wace maman?" "Mamanka mana, bamu taɓa zuwa ba, na san wadda na gani a gidanku ba ita ce mamanka ba" "In ji wa?" Jauhar ta ce "Babu uwar da zata zauna hankalinta a kwance, alhali an yi wa ɗanta sharri an tsare shi". "Mama ta mutu" ji tayi kamar ya soka mata mashi, ta kalleshi ta ce "Kai ma ka san pain ɗin master? Ka girma da ita ka santa?" Ya jinjina mata kai alamar eh. Jiki a sanyaye ta ce "Ni ban ma santa ba, ina yawan takura ƙwaƙwalwata, dan na tunota, da rayuwar da muka yi tare, amma bana iyawa, baba ne yake da hotonta, nayi-nayi ya bani, ya hanani, idan na shiga ɗakinsa zan gyara masa, sai na ɗauki hoton in yi ta kallo ina jin daɗi, duk da ina jin kewarta, ina son in san yaya take ya halinta yake, yadda su mama suke faɗa ne ko akasin haka? Kawai saboda Baba ya saka hoton a cikin wallet ɗin sa, ya ce zai kai a wanko wani ya saka a yi enlarging ɗin sa ya bani, mama ta ɗauki hoton ta yayyaga, ta watsar wallahi ji na yi kamar ta yaga zuciyata, bana riƙo idan an yi mini laifi mantawa nake yi, ana yawan cewa bani da zuciya amma haryanzu a raina, na kasa jin cewa na yafe wa mama abun da ta yi mini. Da farko da na taso, na zata mama ce ta haife ni, daga baya na gane ba ita haife ni ba, sai na fara tunanin ko kawai faɗowa na yi ko tsinto ni aka yi, kowa yana da uwa ban da ni, wataƙila a haka aka haifeni, daga baya na yi tunanin ko kawai 'yar aiki ce ni, na zata 'yan aiki duk ba su da iyaye. Daga baya na gane baba ne babana, uwa ce bani da ita, sannu a hankali kuma na gane ina da uwa amma bata duniyar. Sai dai ba na jin daɗin irin yadda su mama ke aibata mamana, duk da ba ta raye ban san ta ba, har suna cewa mayya ce ta taɓa kama su ma, amma baba yana faɗar cewa mamana mutuniyar kirki ce, irin halina ɗaya da ita, haka yaya saifu ma yana faɗa. Mama ce mariƙiyata, na so in tashi kamar ita ce wadda ta haife ni, amma ƙiriƙiri sai ta nuna mini banbanci ba ita ta haife ni ba. Ta saka aka cire ni daga makarantar kuɗi, aka mayar da ni ta gwamnati wai ba na gane karatu ni daƙiƙiya ce, kuma ni babu mai kula da ni, ko koya mini assignment komai ni nake yi wa kaina gashi baba ba ya iya magana a kan abun da ake yi mini. Ita kuma anty Zakiyya cin zali na zahiri, na daku a wurinta, duk ba wannan ba ni ya riga ya wuce, kawai haryanzu ina jin zafin yaga mini hoton uwata da mama tayi, da ƙazafin nan da suka yi mini, na fanɗarewa, na san zan yafe musu wataran amma ba yanzu ba. Ina son in ga mutum yana hira da mamansa, ko suna wasa irin na ɗa da uwa, abun yana burgeni, ko mutum ya din ga gaya wa mamansa damuwarsa da daɗi master, wataƙila kai ka samu wannan damar ni kuwa ban samu ba, maybe da mamanka ta yi tsawon rai wannan rayuwar za ta zo maka da sauƙi". Tana gaya masa raɗaɗin abun da take ji a zuciyarta yana raguwa, duk da kuka take yi. Ya ce "You are missing her?" Yayi maganar yana kallonta. Ta jinjina masa kai ta ce "So badly" "Ki yi mata addu'a" ta jinjina masa kai tana goge hawayenta, a take shi kuma ya tuna irin tasa rayuwar, duk da lokuta da dama idan ka haɗu da wanda ku ke da irin matsala ɗaya ku ka yi sharing ana samun releif, amma yanzu shi ba ya son doguwar magana idan ya fara ma gajiya zai yi, duk da kwanan nan jauhar na isarsa da saka shi magana, kuma muddin ya gaya mata shi nasa labarin, zata shiga damuwa dan haka ya ƙyaleta. Duk da kuka take yi, ta fara ɗaukarsa a hoto tana murmushi ta ce "Kai zan fara yi wa hoto da wayar nan, haryanzu mamaki nake yi, wai master ne ya saya mini waya, Allah dai ya sanya mini kai a cikin aljanna ya jiƙan mama, ya ja da ran wanda suka rage mana, Allah ya goyi bayanka ya yi maka jagora a cikin lamuranka. Kai master na rasa wace addu'ar ma zan yi maka, na rasa wace irin godiya zan yi maka ma" Har cikin ransa ya ji daɗin Addu'ar da take yi masa. Ya kuma amsa da Amin. "To mun gama ki tafi" "To me na yi maka ka ke korata?" Ya ce "Sigari zan sha" Ta ɓata fuska ta ce "Da sassafen nan ba ka ci komai ba, sai ka fara da hayaƙi, haba mai babban suna, idan a baya babu wanda ya damu da lafiyarka, ni ina son ka yi lafiya, ka rayu saboda ka ajiye 'yar madara, yau dai ɗaya ayi haƙuri dan Allah a ɗaga ƙafa kar a sha da sassafen nan" kamar shashasha haka yake bin ta da kallo, ta karɓe lighter da sigarin hannunsa, har da ta gefe ta cikin kwali ta tattaresu. "Bari na dafa mana shayi, cincin na yi jiya, amma na kasa ci saboda damuwa, ka yi brush sai ka fito ka karya, kuma zan din ga leƙowa saura na ga mutum ya sha wani abu" Sunkuyar da kai ya yi, yana murmushi da gefen bakinsa. Jauhar ta samu na yi, lambar baba ta kira, yana ɗagawa ko gaisawa ba su yi ba ta ce "Baba na yi waya" Baba ya ce "Masha Allah Alhamdilillah, ina tayaki murna waliyya" "Ka hau what's app mu yi video call" Baba ya ce "To shikenan waliyya" Al'amin ya kalleta ya maimaita waliyya a ransa, lallai ta ci sunan da mahaifinta ya kirata da shi. "Master, nan ne wurin video call ɗin ko?" Ya jinjina mata kai alamar eh. Tana kira baba ya ɗaga fuskarsa ta Bayyana a screen ɗin wayar. "Baba wayata touch screen ce mai kyau". Baba yayi dariya ya ce "Masha Allah, Allah ya sanya alkhairi." "Amin, ina su yaya saifu su mama da Anty?" "Duk suna nan lafiya, baba dan Allah kowa da kowa a turo mini lambarsa, duk zan yi musu magana ta what's app, zan din ga kiran su kuma a waya" "To shikenan, a ina ki ka samu waya ne?" "Master ne ya saya mini" sai kuma ta ce "Au amm maigidan ne ya sai mini" Wani irin sanyi ya ratsa zuciyar baba, ya ce "Allah ya saka masa da alkhairi, ya yi muku albarka baki ɗaya" "Amin baba" ta kaste wayar. "Master " ya ɗago ya kalleta. "Na gode sosai" ya ɗan tsuke fuska ya ce "Kin faɗa kin sake, ya isa haka" "Bar ni na yi yabon gwani ya zama dole". Tana cikin maganar hankalinta ya kai kan labarin da ake yi a radio, wata mata ce take kuka, take roƙon gwamna, sarki da kuma jami'an tsaro su kama Aminu mai dogon zamani bisa karya mata ɗa da yayi, ya soke shi da wuƙa, an kai shi asibiti rai a hannun Allah gashi ba ta da ƙarfi, tana neman a bi wa ɗanta hakkinsa. Cikin tsananin tashin hankali, jauhar ta kalli Al'amin, tamkar bai ji me aka faɗa a radiyon ba, sai tauna cin-cin yake yi ƙururus ƙurus ko a jikinsa an mari dutse. Ayshercool 08081012143 32 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955Jiki a sanyaye jauhar ta ce "Master, dama rigima ka je ka yi, ka ji wai a nemoka" Bai tanka mata ba, ya ɗauki kofin shayinsa, ya kai bakinsa. "Dan Allah ka yi magana, menene abun yi yanzu? Ko zuwa zamu yi mu ba ta haƙuri" kallon Allah ya kiyaye ya yi mata. Ta gyara zamanta ta ce "Ka san wani abu? Uwa uwa ce, kuma duk lalacewar ɗanta tana son shi, ba zata taɓa mantawa da kai ba, illata mata ɗa da ka yi, babu faɗuwa a ciki idan mun je mun bata haƙuri, idan dan ɗan wani abu mu bata. Ba yanzu ake ji ba gaba ake ji master, duk rintsi duk wuya kar ka bari wani ya ƙullaceka, sai ka manta ka cutar da mutum, amma nauyin hakkinsa yayi ta ɗawainiya da kai". Ya shanye shayinsa tsaf, kamar a mafarki ta ji ya ce "Alhamdilillah" Ta ce "Masha Allah, Allah ya ƙara mana wadatar zuci da rufin asiri, mu koma waccan maganar master, dan Allah ka yarda mu je mu bata haƙuri" Ƙwanƙwasa gate ɗin gidan aka fara yi, Al'amin ya tashi ya je ya buɗe. Ɗaya daga cikin yaran unguwar ne marasa ji, ya risuna ya ce "Allah ya ja zamaninka" "Ya aka yi?" "Wallahi guduma ne suka yi faɗa da dattijonsa jiya, ya kore shi daga gidan ya ce ya bar masa gida, ya sallamawa duniya shi, shi ne yau ya je ya sha wani abu, gashi can ya kulle mai unguwa a gida, da makami ya ce sai ya sara shi, an kirawo jami'an tsaro an kasa buɗe gidan" Ya ce "Mu je in gani" Suna zuwa gidan mai unguwa suka tarar da mutane cirko-cirko a ƙofar gidan, ga 'yan sanda su huɗu, ana ta fama a buɗe ƙofar gidan an kasa, sai kururwar mai unguwa ta cikin gidan, yana a taimake shi, a raba shi da ɗan sa kan ya kashe shi" Al'amin ya zagaya, ya kama katanga ya dira cikin gidan, ya tarar da guduma a tsaye a ƙofar ɗakin mai unguwa, riƙe da wata sharɓeɓiyar wuƙa, sai ƙyalli take yana dukan ƙofar ɗakin, yana maye yana sai ya kashe mai unguwa babansa. Sauran matan gidan da yara, duk sun rufe ɗakuna suna neman ɗauki. Al'amin ya tunkare shi, yana zuwa ya riƙe shi, ya karɓi makamin hannunsa ya kwaɗa masa mari, hakan ya sa ya ƙara gigicewa, ya danƙo rigarsa ya buɗe ƙofar ya fito da shi sai tangaɗi yake yi. 'yan sandan suka yo kansu, za su kama guduma, Amma Al'amin ya ce "Zamu zo da shi station anjima idan ya dawo hayyacinsa. Mai unguwa da ya tsira da ƙyar ya ce "Ofusa kar ku bari ya tafi da shi, dama shi yake goya musu bayan iskanci a unguwar nan, da ɗa na bai kai haka lalacewa ba, a haɗa a Kama har da shi". Al'amin bai kalleshi ba ya ce "Ko ya gudu ni a kama ni, ba zai gudu ba, idan ya dawo hayyacinsa zan kawo shi da kaina, mu haɗu a station zuwa ƙarfe biyar na yamma ina son a zauna da babansa" "Shikenan, mu na jiranka" Mai unguwa ya ce "Ofusa ya zaka yi mini haka, yaron da ya nemi rayuwata" "Mai unguwa ka jira ya dawo hayyacinsa mu gani, Allah ya kaimu ƙarfe biyar ɗin. Jauhar na wanke-wanke, Al'amin ya turo ƙofa, hannunsa riƙe da guduma, ta tashi tana bin sa da kallo. "Sako hijjabinki, ki kawo mini tabarma" Ta jinjina masa kai, ta sako hijjabi, ta kawo masa tabarma, ya kwantar da guduma, ta ƙare masa kallo ta ce "Wannan ai shi ne ya hana wani ya sare ni, lokacin da na je gida da aka tsare ka" Al'amin ya ce "Kawo mini ruwa a bokiti da kofi" Ta kawo masa ruwa, ya ɗiba ya dinga sheƙawa guduma a ka, ya din ga zabura kamar zai zare, ya ɗaukko gawayi a kurfotin Jauhar, ya daddaka ya kaɗa a kofi, ya matse guduma ya dinga ɗura masa a bakinsa, ya sha wani ya zubo da wani, ya gama ya hankaɗa shi ya kwanta. "Master wai meya same shi ne? Ba shi da lafiya ne?" "Ƙwayar da ta fi ƙarfin kansa ya sha, ya kusa halaka mahaifinsa" Waro ido ta yi ta ce "Mahaifinsa kuma? Subhanallah lamari ya ɓaci" Bayan mintuna arba'in, guduma ya wartsake, ya din ga kallon gidan,  sai da yayi ido huɗu da Al'amin, sai ya ƙara nutsuwa. "Ka farfaɗo?" Guduma ya sunkuyar da kai. "Ka san me aikata ko?" Yayi shiru bai ce komai ba. Al'amin ya yi ajiyar zuciya ya ce "Me ka sha?" "Sigari ce" "Da me?" "Itakaɗai" A fusace ya ce "Zan saka maka ƙarfe wallahi, uban me ka sha ka ke yinƙurin kashe mahaifinka?" "Wiwi ce kawai ban sha komai..... Ba rufe baki ba, Al'amin ya riƙe maƙogwaronsa ya ce "Zaka faɗa ko sai ni na kashe ka?" A rikice jauhar ta ce "Dan Allah Master ka ƙyale shi, kar ka kashe shi" Cikin kakari guduma ya ce "Baƙin capsule ne" "Waye ya baka, kuma waye yake dillancin sa a unguwar nan". "Botorami ne" "Botorami, yaran da suka sareni, na ƙyale shi, shi ne ya fara sayar muku da wannan muguwar ƙwayar? To wallahi sai ya bar unguwar nan. Uban me babanka yayi maka ka nemi kashe shi? Bayan sharrin ƙwaya har da iskanci, uban meyasa ba ka yi yinƙurin kashe kowa ba sai shi?". Cikin damuwa guduma ya ce "Kora ta yayi, ya ce kar na sake zuwar masa gida" "Ba dole ya kore ka ba, tun da abun naka babu hankali a ciki, in anjima zamu je police station, ka bashi haƙuri, idan kuma ka bari yayi maka baki, ka shirya lalacewa da taɓewa fiye da wadda ka ke ciki yanzu" ya jinjinawa Al'amin kai. Al'amin ya ce "Ka zauna a nan kar ka fita ko ina" Jauhar mamaki ta din ga yi, dama Al'amin ya san abun da ya dace, amma shi yake wanda bai dace ba. Jauhar ta gama abincin rana, ta zuba ta bawa guduma, ya karɓa ya ce "Ya gode" Al'amin ya zaunar da shi yana yi masa tambayoyi, sai dai bayanin da ya yi wa Al'amin, a kan irin rayuwar da ya tashi a kai, gaba ɗaya jikin jauhar yayi sanyi, wato wasu lokutan mutane na yin gaggawar yankewa wasu hukunci, ba tare da sanin ainihin abun da ke ɓoye ba. "Da la'asar suka tafi police station, tun da suka je mai unguwa yake bala'i, har da cewa 'yan sanda su kama guduma su yi masa duk abun da za su yi masa shi yafi ƙarfinsa. "Uwarsa ce ta lalata shi, sannan ta dawo mini da shi, baya sana'r komai sai shaye-shaye na tsiya da ya ɗorawa ransa, yau kuma rayuwata yake nema, to wallahi ba a haifi ɗan da zai kashe ni ba, waccan shashashar uwar ta sa ita ce silar komai, bayan ya lalace ta nannaɗo ta kawo mini shi" Al'amin ya ce "Ina mamakin yadda aka bawa mutum irinka jagorancin al'umma alhalin ba ka iya jagorantar gidanka ba. Kai da ka haife shi, baka iya bashi tarbiyya ba hukuma ce za ta tarbiyantar maka da shi? Ka san ba zaka iya kula da shi ba meyasa ka haife shi? Da ka saki majaifiyarsa ka maye masa gurbinta? Sakinta ka yi ka bar mata shi, ba ka san cin sa da shan sa ba, balle iliminsa da lafiyarsa, baka nuna masa sana'a ba, baka bashi jari ba, ita ba cikakken ƙarfi ba itakaɗai tayaya zata iya yi maka rainon ɗa? Ka san jikinka yana buƙatar ka auri mata barkatai, ka yi jima'i ayi ta haifa maka 'ya'ya amma ba ka tunanin inganta rayuwarsu, ko buƙatar ka kawai ita ce buƙata?" "Kaga Al'amin ya isa hak.... Al'amin ya ɗaga masa hannu ya dakatar da shi, ya cigaba da magana. "Babu in da za shi, tun da ka haife shi, dole ka kula da shi, ka yi masa role ɗin uwa tun da ka saki uwarsa a lokacin da ya fi buƙatar ku rayu tare, idan ba haka ba ko ba shi ba, a cikin wannan tulin 'ya'yan zaka samu mai halaka ka. Ya mayar da idonsa kan Guduma ya ce "Kai kuma ya muka yi da kai?" Guduma ya durƙusa ya ce "Baba dan Allah dan Annabi ka yafe mini, ka yi haƙuri ba zan sake ba in sha Allah, dan Allah ka janye korar da ka yi mini daga gidanka, nayi kuskure ka yi haƙuri " Sai dai mai unguwa yayi tsit, dan kuwa Al'amin ya gama kwaikwaye shi a gaban mutane, yayi mamakin maganganun da suka fito daga bakin Al'amin ɗin. "Officer, zan kawo yaron da yake sayar da wannan capsule ɗin, a riƙe shi a matsa shi, ya faɗi ina yake samota" ya sake kallon guduma ya ce "Ka shelanta, cikin unguwar nan, duk wanda na kama da sayar da irin wannan nau'in kayan, sai na lahira ya fi shi jin daɗi" Ya jinjinawa Al'amin kai. "Yanzu dai ina nema masa afuwa, yayi nadama in sha Allah ba zai sake ba". "Idan ya sake fa, ni fa gaskiya rayuwata tana cikin hatsari" "Ayi rubutu, duk abun da ya yi zan ɗauki laifin" Ba mai unguwa ba, har Guduma Nura sai da ya kalli Al'amin. Aka yi sulhu da rubuce-rubuce, suka fito, guduma ya risuna yana yi wa Al'amin godiya. "Manta, mu je ka rakani asibiti, kan waccan uwar mitar ta sakani a gaba" Guduma ya ce "Antynmu ayi mata godiya, abinci yayi daɗi na gode master" bai ce komai ba, suka tafi asibiti. Ko da suka je emergency, Al'amin har gaban gadon yaron da ya karya ya je, ya tarar da shi a kwance, ana saka masa ruwa. Yana ganin Al'amin ya rikice, ya yinƙura zai ɗago, Viper ya mayar da shi, ya kalle shi ya ce "Na ji babarka na kururuwa na nakasta ka, a ɗaukar mata mataki, kai ba ka gaya mata babu mai iya ɗaukar mata mataki ba? Yanzu ka dawo hayyacinka ka tuna abun da ka yi ko? Ba ka sanni ba ko? Saboda ka sha ta gaya maka ƙarya, ni ka tunkara zaka sara ko? Wai ba kai ne ɗan mama ba, da aka rufe kwanaki madaki ya saka ka kashe wani yaro a dabarku ba? Ya shiga ya fita an sake ka, yanzu kuma da ka nakasa ya kasa taimakon ka ko?". Ya sunkuyar da kai ya yi shiru. "Za a zo a biya kuɗin maganinka, nan gaba ka sake zuwa ka tari gaban tirela, ta kanka zan bi" Ya kalli guduma ya ce "Tashi mu ware" Ya tashi suka tafi, kamar wa da ƙani, suka bar mai unguwa da kunya. Bayan fitar su Al'amin, jauhar ta kaiwa telar da take yi wa aiki kaya, ta rage mata wani abu a cikin kuɗin, amma ba ta bata duka ba. Ta tarar da yaran matan layin, suna ta bajekolin magungunan mata, ana ta shewa. "Jauhara ba za ki sayi abun arziki ba, ga kaya nan sai wanda ki ke so, kuɗi kuɗi iya kuɗinki iya shagalinki" Kawai tayi murmushi ta basar da su. Wasila ta ce "Wai sai an yi magana sai ki wani din ga mazewa kamar baki san komai ba? Ke an daina irin wannan abun kamar a zamanin da, idan baki zanzare kin fitsare ƙafafuwanki ba,bar ganin mijinki a haka ba ruwansa da kowa, wallahi sai ki ga ya fara 'yan leƙe-leƙe, ki zo ki ɗauki gyara hajiyata, ita mace sai d gyara, wannan kyan fuskar ta ki ba shi kawai yake so ba" Jauhar ta ce "Hmm Anty wasila kenan" "Ba wani anty wasila, malama ki rage maƙo dan Allah, kin iya neman kuɗi sai aukin saka turaren wuta a gida, da goge goge, amma ba zaki sai kayan gyara ba, ina ta tallata miki kayan maman neehal ɗin nan, baki ga kyan su ba, amma sai ki yi burus". Suwaiba tela ta ce "Wai wasila ki ƙyaleta mana, ki ka sani ko tana abun ta, idan tana yi gaya miki zata yi?" "Ba wani, ni fa jauhar ƙanwata ce, ƙanwa na ɗauketa, kunyarta tayi yawa Allah ya sa ba haka ki ke yi masa ba, babu yadda za ayi ki je ki ganta da shirt da wando, sai uban hijjabi da dogwayen riguna kamar zata yi ɗawafi. Ki tsuke ki ci zamaninki tun da ƙuruciyarki, ni ga wani tsumi nan na baki, na maman neehal ne, tested and trusted, ki gwada zaki bani labari. (0706 677 4630 ga lambar da zaku samu maman neehal, domin samun kayanta) Kamar sokuwa haka Jauhar ta karɓa, kasancewar ta san ba wani amfani da zai yi mata. A gurguje ta kammala abun da za ta yi a gidan, ta fito saboda irin manyan karatun da ta ji suna yi, da suka fi ƙarfin kanta. Ta koma gida, ta din ga kallon robar abun da anty wasila ta bata, na wurin Anty lubabatu ma suna nan, ko kallonsu ma ba ta yi. Aka fara kiraye-kirayen  sallar magariba, tana salla, ƙarar wani babur ya cika mata kunne, bayan ta idar tana cikin lazumi, ta ji ana kokowar shigowa da abu, ta tashi ta fito tsakar gida, ta tarar da Al'amin yana shigowa da wani tsohon babur jincheng, hannunsa riƙe da salansar babur ɗin. "Master, wannan kuma fa?" "Jaki ne" ya bata amsa. "Wai sai ka yi ta gaya mini baƙar magana, wai ko shi ne ya cika layin nan da ƙara?" "Eh" "To meyasa ka cire masa salansa? Ka ji ƙarar kuwa ba daɗi, kamar ya shekara ba a kunna ba". Ya jingine salansar, duk ya ɓata jikinsa da baƙin mai, ya ce "Na fi son sa a haka" "To wai a ina ka samo babur?" "Sata na fara" yayi maganar zai shigar mata falo. Ta ce "Allah ya baka haƙuri, amma tsaya na kai maka ruwa banɗakin tsakar gida ka yi wanka, idan ba haka ba zaka ɓata carfet ɗin da baƙin mai".. "Naɗe abun ki na wuce, ba zan yi wanka a tsakar gida ba" Ta shagwaɓe ta ce "Ba fa a tsakar gida ba, toilet ɗin tsakar gida". "Ƙoƙarin shiga falon yake, tayi sauri ta ɗaukko tsumma, ta durƙusa ta ce "Bari na goge maka, kar ka ɓata mini carfet" ta gogge masa, sannan ya shiga. Warin sigarin da yake yi ya sanya ta bin sa da ruwan zafi, ta matsa masa toothpaste a kan brush, ta ajiye masa. Allah ya taimake ta, babu musu yayi wanka yayi brush, ya fito yana goge jikinsa, ya buɗe wardrobe ta shigo da sauri ta ce "Saura ka watso mini kaya ƙasa, na sake gyarawa, nuna mini wanne zaka saka na ɗaukko maka?" Ya nuna mata, ta ciro masa su, kafin ya karɓa ta miƙo masa kwalbar turare ta ce "Ka shafa turaren, sai ka saka" Haɗin da take amfani da shi ne, ta daka alumun, da farin muski na gari, da kanumfari,  ta dafa su suka tsumu ta ta ce, ta zuba madarar turare a ciki. Ya karɓa ya shafa, ya miƙa mata, ta karɓa ta ce "Ai naka ne, na bar maka" Ya karɓa zai ajiye, ta ce "Baka ce ka gode ba" sai ya miƙo mata abun ta, da ya ce ya gode gara ya dawo mata da abun ta. Tayi dariya ta ce "Hukuma sai da rarrashi, na janye ba sai an yi godiyar ba" Ya ajiye, ya fara ƙoƙarin saka kayan, ta fita ta bashi wuri, shi kansa ya ji daɗin jikinsa sosai da sosai, ga ƙamshin yayi masa daɗi sosai da sosai. Ya fita ya kame a falo, ƙamshin turare sai ɗibarsa yake yi. Akwai English wears a cikin kayanta, sai dai ba ta taɓa gwada sakawa ba, dan kunya ma take ji, domin kuwa sai kwanan nan ta daina yawo da hijjabi a cikin gidan. Da ƙyar ta iya fitowa da doguwar rigar atamfa, da ta ɗan kamata cif jikinta, ta zo ta zauna a falon, ta ce "Master ya ku ka yi a police station kuwa?" "Labari zan baki ko yaya?" Ta ce "Eh mana" "Kunna radiyonki, ki ji labarai idan shi ki ke son ji". Cikin shagwaɓa ta ce "Ni naka nake so" Ya ce "To ni ban san me zan ce ba" Ta ce "Ai shikenan" "Yauwwa, na ce ba ka ga azumi saura 'yan kwanaki, yakamata ace ko sugar da lemo mu saya mu je mu gaida su Abba" "Sai kin dawo" ya faɗa yana shan kunu. "Master meyasa?" "Kawai". "Na san akwai dalili, amma koma menene ka yi haƙuri, ba a fushi da iyaye, kai fa ka gama yi wa wani nasiha ɗazu, meyasa ba zaka yi amfani da ita a kanka ba?" Juya mata baya ya yi, irin idan kin gama kya yi shiru. Zuciyarta cike da fargaba, ta taka ta je kusa da shi ta zauna ta ce "Masu sunanka manyan mutane ne, dattawa, ba sa haka, dan Allah kar ka saka mu shiga fushin Allah, iyaye ba abun watsarwa bane ba, ranar da babu su da kuɗi ba zamu gansu ba, mun rasa iyaye mata, mazan sai mu nemi albarkar su" Ya ɗaga hannunsa ya ɗora a kan kunnensa, ta kalli dogwayen yatsunsa, faratansa sun yi tsayi. "Gobe in Allah ya kaimu friday ce, a yanke farce, sumar nan ma tayi yawa yakamata a rage ta, ayi maka gyaran fuska kafi kyau idan aka aka rageta" Juyowa yayi gaba ɗaya, ya ƙureta da idonsa. Sai jikinta yayi sanyi, tsigar jikinta ta tashi yarrr. "Kin fa dame ni" yayi maganar a hankali, amma muryar da yayi amfani da ita, har cikin zuciyarta. "To me nayi maka na takura?" Shiru yayi bai yi mata magana ba, ya cigaba da ƙare mata kallo. "Baka saka mini lambarka a wayata ba" Ya miƙa mata hannu, ta bashi wayarta, ya saka mata lambarsa, ta ce "Yauwwa na gode, zan din ga yi maka flashing, kamar sau arba'in a rana" "Iya arba'in?" "Eh, ko yayi kaɗan?" Ya girgiza mata kai alamar a'a. "To ɗan yi mini downloading ɗin game" Ya ce "Sai kin gama jarrabawa tukuna" "Ai mun kusa in Sha Allah" ya lumshe idonsa ya ce "Allah ya bada sa'a" "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum master, 'yar madara na godiya" Ta sake cewa  "Dama wainar fulawa zan yi mana mu sha da tea, bari na ɗora" Ta fita tsakar gida, ta hura kurfoti, ya biyo ta gaban kaskon ya zauna, sai dai kallon da yake yi mata duk ta takura. "Master, kamar fa akwai ɓera a gidan nan, dan Allah ka sayo maganin ɓera" Ya ce "Shi ma tsoron nasa ki ke ji kenan?" Tayi murmushi ta ce "Eh, amma ba sosai ba" "Ya haɗa nasa shayin, tana soya waina yana cinyewa" "Master ban gane ba, idan ka cinye ni fa?" "Sai ki soya wata" "Ko kuma ka soya mini ba, ƙullin fa bashi da yawa, ka ƙoshi gaskiya" ta janye plate ɗin. Ta gama ta haɗa nata tea ɗin, ta fara ci. Ya zuba mata ido, cin abincin ma yanga take yi masa. Yana zaune yana kallonta, ta gama ta haɗa wanke-wanke ta yi. Ta gama komai, zata shiga ɗaki ta ce "Na gama taso mu tafi, kar sauro ya saka maka zazzaɓi". "Dama na ce miki ke nake jira ne?" Jauhar ta ce "Eh dole ka ce haka, tun da na cika maka cikinka, aishikenan sai da safe, dan Allah kar ka sha komai ka ji master". Yayi mata shiru, ta ce "Master, magana nake fa, na san kana ji na, dan Allah kar ka sha komai ka ji Mai zamani" Ɗagowa yayi ya kalleta, tayi masa murmushi, tasowa ya yi, ya biyo bayanta. Tsayawa tayi ta ga me zai yi mata. Yana zuwa ya riƙe kunnenta ya ce "Me ki ka ce?" "Master na ce" "In kuma jin kin faɗi wannan sunan, zamu gauraya da ni da ke" sai dai duk wannan abun fuskarsa ba fara'a. Cikin shagwaɓa ta ce "Kunnena zai cire fa" ya tura ƙeyarta, har ƙofar ɗakinta, ta ce "Kar in sake ganinki sai gobe in Allah ya kaimu". "To na ji, amma dai kar ka sha komai dan Allah" wucewa yayi ɗakinsa, ta ƙarasa gaban gadonta tana murmushi. Ta yi wanka, ta shirya ta shafa turarukan ta, ta nemi wuri ta kwanta. Sai murmushi take yi, tana jin daɗin cigaban da ake samu a kan zaman su. Ta kalli pillown da take rungume da shi, ta shafi pillown a hankali, tana tuna hirarrakin da aka yi ɗazu da su Anty wasila. Tabbas abun da take ji game da aure ya sha banban da abun da ta tarar, to ko ba haka abun yake ba? Sai kuma ta tuna har a littatafan addini ta karanta. Hakan yana nufin Al'amin ba shi da lafiya ne? Ko kuma ita ɗin ce ba ta gabansa, sai dai ya ci, yayi shaye-shayensa ya je yawonsa, ko kallon kirki ba ta ishe shi ba. Tunani take yi ko dai tana da wani naƙasu ne, da ya sanya ba ta gabansa, ko da wasa bai taɓa ko makamancin yi mata wani abu ba. Ta yi juyi ta kalli gadon, yanzu idan Al'amin ba shi da lafiya ne, ko bashi da ra'ayin hakan, haka za su cigaba da rayuwa kenan, ita ba kowa ne da ita balle su tattauna, ko da wasa kuma ta san ba zata tunkare shi da wannan maganar ba, ko ta kai masa kanta, wannan ma ba mai yiwuwa bane ba. Wataƙila wani babin ne na ƙaddarata. Ta faɗa a zuciyarta, a lokacin da bacci yake ƙoƙarin awon gaba da shi. Misalin ƙarfe uku da rabi na dare, wani matashin saurayi ne, yana ta kai komo a tsakanin wasu gidaje can wajen gari, da alama wani abu yake jira. Wani mutum ne ya zo a keke, ya tsaya ya kalle shi ya ce "Nan ce sabuwar mahaɗarmu?" Mutumin ya amsa da "Eh, kuma ka yi taka tsantsan, kar a gane, kar kuma ka yadda da kowa" "To shikenan, yanzu zan je na rarrabawa gayu kayan, ga wannan balance ɗin jiya ne" yayi maganar yana miƙa masa kuɗi, mutumin ya karɓa, shi kuma ya tafi. Sai dai ya nufi in da yake son tafiya, ya ji an danƙi jijiyar wuyans, a take ya sulale sumamme. Suka ɗauke shi suka tafi da shi, Walid ya kira Al'amin ya ce "Maganarka haka take mai dogon zamani, mun kama yaron nan, ka san yaron madaki ne ya rarraba musu ita, idan ban yi kuskure ba madaki yana cikin manyan dilolin capsule ɗin nan. "Ku shigo da shi cikin unguwa, ku ɗaure shi, ɗauri na gasken gaske ku bar shi, zan yi magana da 'yan sanda" "To shikenan, amma ka din ga yi kana ankarewa da hankakin nan ka san ba mutunci suka cika ba" "Ina ankare, sai da safe" Har ƙarfe tara na safiya, Al'amin ya je yayi sabgoginsa ya dawo, jauhar bacci take yi. Ya tsaya a ƙofar ɗakinta, yana ƙwanƙwasawa, a hankali ta yi juyi, ya ɗaga labulen ya ce "Ba a san gari ya waye ba ne? Yunwa nake ji" "Afuwan gani nan" tayi maganar cikin muryar bacci. Da kayan jikinta ta fito falo, gashinta duk a hargitse ta ce "Yi haƙuri, baccin nawa ne yayi nauyi". Ta tarar ya sayo gasara, ya sayo awara ɗanya. Mamaki ta din ga yi, a ina ya san ana sayarwa, amma tafi yadda aikawa yayi a sayo masa. Ta shiga ɗakinsa gyarawa, ta buɗe wardrobe ɗin sa, kayan da ya cire jiya ta tattara zata wanke, ya kwasa ya mayar da su cikin wardrobe ɗin, kayan dai da ba ta so, sai da watso su, ya ɗauki abun da zai ɗauka duk ya cukurkuɗa su ya mayar cikin wardrobe ɗin. Yana ganin ta tsaya tana kallon wardrobe ɗin, yayi waje dan ya san mita za ta yi. Ta kuwa biyo shi falon "Master, yanzu duk gugar da nayi ka wargazata, ka haɗa mini wankakkun kaya da marasa wanki, har da jiƙaƙu duk ka gwamutsa mini su a ciki" tayi maganar kamar tayi kuka. "Ke fa ki ka ce, na daina zubar miki da kaya ko ina a cikin ɗakin" "Kuma master kaya kala ɗaya da zaka saka, sai ka hargitse ilahirin wardrobe ɗin? Zan samo maka bagco, ka din ga zuba marasa kyau a ciki, dan Allah ka daina hargitsawa" yayi mata shiru, ta gama mitarta ta gama, tana komawa gyarawa ya dafe kai, ta gama mitar kuma ta gyara. Sai da ya tabattar ta fita daga falon, tana aiki a kitchen ya ɗaga wayarsa yayi kira. "Kuna aikin da na saka ku?" "Eh muna yi" "Kar ku kuskura ku bari wani ya kwance shi, idan ba jami'an tsaro ne suka zo ba" Ya gama karyawa, yana son ya tashi ya fice, ta tistiye shi da zancen yanke farce, haka ya koma ya zauna, ta saka reza ta yanke masa farce tsaf, tana yi tana yi masa surutu. Baya son ta gane ya yi wata tsiyar a waje, kar ta zauna ta yi ta masa kuka. Ta yi masa gugar kayan da zai saka, wai ya tafi masallacin juma'a, shi rabonsa da zuwa sallar juma'a har ya manta, yayi wanka ta bashi goggagun kaya, ta shafa masa turare ta ce "Ka dawo da wuri dan Allah, ina gama abinci ka ci da zafinsa, ka yi mana addu'a idan ka je" Ya gurgura babur ɗin sa da ya cire wa salansa, ya fice ya cika layin da ƙara. Daji ne sosai babu gida a gaba, babu a baya, daga shi sai direbansa suke tafiya sai P.A, har suka ƙaraso wurin wani dutse, suka sauka da shi da P.A, suka tattaka har gaban bukkar. Cikin bukkar tamkar fadar mahaukaci, duk an yi mata ado ƙahunhuna da ƙwarangwal ɗin dabbobi, har da wasu sassa na ƙashin ɗan Adam. Gefe ga wani mutum na tsurut, kamar an fato shi, jikinsa ko riga babu, daga shi sai wani ɗan warki ɗaure a ƙugunsa. Suka nemi wuri suka zauna, ya kalli indabo ya ce "Aikin farko yayi, wa'adin da muka ɗiba maka yau ya cika, aljanu sun sha jini a ƙasar da suka buƙata. Saura mahaɗin aiki na biyu, za a samo matashiyar yarinya, matar aure shekara sha biyar zuwa sha takwas, zaka kasance da ita, tsawon kwanaki uku, a ketowar alfijir ɗin kowace rana, zaka fara aikin a larabar tsakiyar wata, shi ne sa'ar aikin! An ɗeba maka wa'adin kwanaki Arba'in ba biyar" Ayshercool 08081012143 33 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Jinjina kai indabo yayi, ya ce "Za ayi ba zai gagara ba, zamu dawo idan an kammala aikin, kuma wa'adin da aka ɗibar mana ya cika". "Shikenan, nasara tana tare da kai, ba yaƙini muke da shi ba, tabbaci nake bakaz duk da akwai ƙalubale a gaba, sai da ba za su gagara ayi maganin ƙalubalen ba, amma a gaba kaɗan ɗin akwai dutse, da zaka yi karo da shi, na buga na duba, duk babu hanyar maganin dutsen nan, sai dai ayi ragas, ko ka kar dutsen ko ya kar ka" P.A ya ce "Kuma babu yadda za ayi da dutsen? Ko wata mafitar?" "A yanzu dai babu, Suka tashi suka fito, suna tafe a hanya Indabo ya ce "P.A" "Na'am honorable" "Bokan nan kullum cikin faɗin ayyuka masu hatsarin gaske yake, ina tsoron tonuwar asirina, kar mu je in sake janyo wa kaina jagwal kana kallon yadda yarinyar nan Naja'atu ta zame mini alaƙaƙai" "Mu bi komai a sannu sir, zamu yi nasara kuma samo yarinya ba zai gagara ba, ko cikin ƙauyukan nan aka bincika za a samu, ko kuma Naja'atu ta samo a irin mutanen da ke hulɗa da su" yayi ajiyar zuciya ya ce "Ba zan so ce a samo ta ɓangaren ta ba, amma kai na ɗora maka ragamar samowar" "Za a bincika in sha Allah sir" "Yayi, ina jiranka, ka ga idan lokaci ya ƙure, aikin da muka yi ya koma baya" "Haka ne, da yardar Allah ka ci kujerar nan ka gama, mu je injiniyoyin suna can gida suna jiranka, aje ayi lissafi" "Ok to, Aminu haryanzu ya ƙi zuwa ko?" "Wallahi yaƙi, Allah da wani wanda zai iya yi mana irin kasadar da yake ɗauka, da mun canza shi, ɗan rainin hankali ne, ko fushi yake saboda wannan karon ba ka fito da shi ba?" "Da fushi yake yi, ba zai ɗauki wayata ba, kuma ina son aiki da shi, ba ya jin kasada komai zafinta kuma ba shi da mgana ko kisan kai zaka yi a gaban sa, sai ya ga dama zai ɗaga kai, balle ka ji zancen a waje. Sannan babban abun shi ne, bokan nan ya ce nasarata tana tattare da wanda yake zubar mini da jini, na riƙe shi sosai, shiyas nake shanye iskancin sa". P. A ya ce "haka ne ya na da amana, ba shi da magana sam, amma shi ya san da hakan ne?". "Haba dai, hauka nake yi na bari ya sani, ba abun da ya sani, kawai aiki yake yi mini" Misalin ƙarfe huɗu da rabi na yamma, manyan injiniyoyi ne zaune a falon indabo, suna ta lissafin ginin plazarsa. Ga wanda zai tattauna da su a kan harkar yaƙin neman zaɓensa, suma su na jiransa. Al'amin yana cikin falon, ana ta lissafi, shikuwa yana hakimce yana kallon tv. Sai da aka gama lissafi, za ayi total ɗin kuɗi, Al'amin ya kalli shugaban engeneers ɗin ya ce "Kayi plusing da kuɗin siminti buhu shida, da tiles carton biyar" Ya ce "Na menene?" "Ina ruwanka, ka saka kawai". Injiniya ya kalli Indabo, Indabo ya ce "Kuɗi ka ke buƙata ne na baka?" "Gyaran gidana zan yi nima" Indabo ya ce "Engeneer a rubuta, a bashi" Al'amin ya sake cewa "Akwai yarana mutum biyar, da nake son a saka mini su a cikin aikin ginin nan, su yi su ma a sallame su" P.A ya ce "An gama mai dogon zamani" "Zamu zo tare da su, ni ne cikon na shida, da ni za ayi aikin a biyani" P.A ya sake cewa "Ba ka da matsala" Aka gama aka sallami injiniyoyi, 'yan jami'iyya suka shigo, duk yana zaune, aka gama meeting. Duk sai da suka gama, sannan Indabo ya mayar da hankalinsa da Al'amin ya ce "Mai zamani" ya ɗaga ido ya kalli indabo. "Akwai tafiya da zan yi ƙaddamar da takarata, a yammacin garin nan, ina buƙatar tawagar ka kai da mutanen ka, saboda ban san ya zata kaya a wurin ba, 'yan sandan nan gaibu ne wasu lokutan". "Yaushe ne?" "Nan da kwana goma" "Cikin azumi kenan?" Indabo ya ce "Eh" "Allah ya kaimu, baka da matsala" P.A ya ce "Allah ya ƙara maka nisan zango mahadi mai dogon zamani. Ina matarka kuwa?" Da sauri ya kalli P.A ya ce "Kamar ya ina matata, meye haɗinka da ita?" "A'a babu komai, lokacin da kana tsare ne, ta zo ita da Walid, ko da yadda za ayi ka fito, lokacin honorable baya nan" Viper ya yi shiru bai sake cewa komai ba. Wata ƙatuwar mage ce ta shigo, da matasan 'ya'yanta, fara tas kana ganinta ka san 'yar waje ce. Al'amin ya tashi ya nufi in da take, ya saka hannu ya ɗauki guda ɗaya ya ce wa P.A "Wannan mace ne ko namiji?" "Namiji ne" "Zan tafi da shi" P.A ya ve "Ka san kuɗin abun nan kuwa? Ya kai dubu ɗari shida fa, wannan ƙaramin". "Da gold aka yi shi ne?" Yayi maganar yana nuna ɗan muzurun da yake ta ihu saboda ya ji matsa. Indabo ya ce "A'a ɗan Germany ne" "Tun da ba daga aljanna ya zo ba shikenan, kai kawo leda na saka shi" yayi maganar yana kallon mai goge-goge. "P.A ya ce wace irin leda kamar zaka ɗauki masara, kwando dai za a baka. Yayi ƙerere, aka kawo masa kwando, ya saka muzurun ƙato da shi fari, jikinsa cunkushe da gashi mai kyau. Ya kalli Indabo ya ce "Zan tafi" Indabo ya yi murmushi ya ce "Ga abun kuɗi nan ka ɗauka a hannunka, ai ba sai an sallameka ba" "Za a sallame ni ko in tafi?" "P.A sallame shi" P.A ya buɗe jaka, ya ɗebo kuɗi ya miƙawa Viper. Al'amin yayi masa wani mugun kallo, indabo ya ce "Ƙara masa" "Ya ƙara ɗebowa, ya ƙara masa" Ya karɓa ya ce "Na karya wani yaro, yana emergency, babar yaron tayi maganar a kamani, a bi wa ɗanta hakkinsa, yana can a emergency asibitin tsakiyar gari, a kashe wutar, ko ta ƙone yiwuwar aikinka, hankakin nan suka yi ram da ni, ba zan yi aikinka ba" daga haka ya fice daga falon. P.A ya ce "Kai, honorable Mai zamani yana hawa kanmu da yawa wallahi, wai sai abun da yake so za a din ga yi yayi ta yi wa mutane tunƙaho?" Indabo yayi murmushi ya ce "Rabu da shi lokaci ne, bari a ci zaɓen, ai ka ga mutumin can ya ce akwai nasarar mu a tattare da shi, yanzu abun da za ayi, ka koma ka yi waya, ka saka a haɗa wata tawagar ta 'yan daba, da zasu far mana a wurin taron, yadda za a samu a zubar da jinin shi ma a can. Sannan ka tara mana 'yan media, idan hakan ta faru a ce abokan adawa ne suka yo hayar 'yan daba suka far mana". "An gama honorable, yanzu kuwa zan je na tara su na sanar musu tun yanzu" "Yauwwa, idan ka gama da su, a hanzarta ko aike ka yi wurin wanda ya karya ɗin, a rufe bakin babarsa" "Ok sir" *** Al'amin ya koma gida, ya tarar da Jauhar da maƙwabta, tana yi musu kitso. Yana shigowa hannunsa riƙe da ledoji, ta tashi tana murmushi, suka gaishe shi, babu wanda ya amsa sai sannu zuwan da tayi masa ya amsa. Ta miƙe hannu za ta karɓi kwandon, ya ce "Banda wannan" ya shiga falo da shi. Ta dudduba kayan, kayan abinci ne wata irin ajiyar zuciya ta sauke, tare da yi wa Allah godiya. Allah ya sa ta gama kitson, ta sallame su suka tafi, ta shiga falon hannunta riƙe da cup ta risuna ta miƙa masa. Ya karɓa ya ga zoɓo mai sanyi, sai ƙamshi yake yi. Ya kafa kai ya zuƙe ya miƙa mata kofin ta ce "Ba ka ce ba" Ya ce "Alhamdilillah" tayi murmushi ta ce "Sannu da zuwa" ya jinjina kai ta ajiye kofin, ya jefo mata muzurun nan a jiki, ta saki ihu tana tsalle, ta ce "Meye wannan?" "Shi ma wannan ɗin tsoronsa ki ke ji?" "Kamar kare fa?" "Mage ne, saboda ƙadangarun da suke damunki, ko shi ma tsoronsa ki ke ji?" Ta ce "Laaa, to ai bai yi kama da mage ba, masha Allah so cute" ta durƙusa ta ɗauke shi. "Master ina ka samo shi dan Allah, kamar ba ɗan nan ƙasar ba. Kai amma na ji daɗi sosai, wani sunan zamu saka masa" Ya ce "Muzuru" Ta kwaɓe fuska ta ce "Muzuru kuma? Sunan gayu za a saka masa, wane irin muzuru?". "Ba sunansa kenan ba?" "A'a, na saka masa suna mai zamani" "Ki ka kuma ko?" Yayi maganar yana kallonta. Tayi murmushi tana shafa kyakkyawan jikin muzurun. Ya ve "Da gaske kin je wurin P.A ɗin Honorable lokacin da aka rufe ni?" Ta kalleshi ta sunkuyar da kai. "Ki bani amsa" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Ko wani irin hali zan shiga, kar ki sake zuwa wurin wani, mussman gidanmu da wurin 'yan siyasar da nake mu'amala da su, dan su fito da ni" Ta ce "In sha Allah, ba zan sake ba, amma dan Allah ka daina zuwa wurin da zaka cutu, kaga idan aka rufe ka, nikaɗai nake damuwa ba wanda yake taimaka mini, ni kuma ba zan iya jurewa ba ganinka a tsare" tayi maganar jikinta a sanyaye. Ya saka hannu a aljihunsa ya ciro kuɗi, ya ce "Ungo" Ta saka hannu ta karɓa ta ce "Na menene master?" "Ana zubar da kuɗi ne?" "Wai bani ka yi? Duka nawa ne?" "Mmm ki sha madara" Ta washe baki ta ce "Allah ya saka da alkhairi, Allah ya yi maka jagora, ya ƙara jan dogon zamanin nan" Ya ce "Za ki ga zamani, idan na kamaki" Tayi murmushi ta ce "Wannan kuɗin ya fi ƙarfin shan madara ai" Ta din ga kwarara masa addu'a, tare da nuna tsantsar farincikinta a kan abun da ya yi matan. A daren ya kira guduma a waya, ya sanar masa da batun aikin ginin da za ayi, ya kira Walid da su liti, da wasu daga cikin yaransa, sai dai sai da suka sha wiwi, suka yi bushe-bushen su, domin samun ƙarfi wurin gabatar da aikin. Sai dai tun da Allah ya sa Al'amin ya kawo ɗan muzurun nan, jauhar ta samu nayi, ta tattara nutuswarta da hankalinta a kansa. Duk ranar da babu aiki, sai guduma ya zo gidan Viper, ya tambayi jauhar ko ta na da aike ta kawo ya kai mata, tun ranar da ya ga zata kai markaɗe, ya karɓa ya kai mata, Anty sama Anty ƙasa, kasancewar ta mai kyauta, ya sanya take farinjini a wurin mutane, dan idan yayi mata aike, idan tana da Abinci ta na bashi, ba da abincin nan ba ƙaramin kankaro mata kima yake yi a. Sai guduma ya mayar da Al'amin kamar yayansa, bashi kaɗai ba, har 'yan sauran yaran da suke rashin jin, jama'ar guduma, idan suka ga Al'amin, tsakaninsu da shi girmamawa, idan da kuɗi a jikinsa, haka zai bi su mai ɗari biyar mai dubu, hakan ya sa suke yi masa biyaya sosai da sosai. Hatta layin gidansa, idan kwata ta cika, ko ciyayi suka fito, haka za su zo da kayan aikin su, su gyara tsaf. Sannu a hankali, Al'amin ya fara janye matasan, shi dai ba zai hana su shaye-shaye ba, sai dai akwai abubuwan da ya yi musu iyaka da sha. Da sharuɗan da ya gindaya musu, a kan in dai za su zauna da shi, sai sun kiyaye su. Jauhar tana makaranta jarrabawa, biyu suka yi ranar, ta dawo ta tarar an yi plasta a gidan gaba ɗaya, da shi da su Walid da guduma, sun yi kaca-kaca da gidan. Tana tsaka da mamakin ya dawo, ya tarar da ita ta ce "Master, aiki ku ka sha haka? Baka gaya mini ba, balle na kwashe kayan kuma ayi wa masu aikin girkin?". "Da su mai laya muka yi, ba wani abu". "Master wai a ina ka samu kuɗi haka? Amma ka yi haƙuri idan tambayar da na yi tayi tsauri". "Bana sata" amsar da ya bata kenan ya fita. Zata iya shaidar hakan, amma yakamata ace ta san in da ya samu kuɗi, tana tsoron ya ɗaukko musu rigima, sai dai gidan yayi kyau sosai. Da daddare ya dawo, sai dai sai wani share ta yake yi, dan ya ji haushin tambayar da tayi masa. "Master, dan Allah ka yi haƙuri, na san tambayar da nayi maka tayi tsauri, amma ka yi haƙuri dan Allah, Allah Ya ƙara maka arziki da wadata, ya tsare mini kai a duk in da ka ke" yayi mata shiru yaƙi amsawa. "Tuba nake, tare da dukkanin girmamawa kaina bisa wuyana, nake roƙon ayi mini afuwa, ayi haƙuri a yafe wa ƴar madara ranka ya daɗe, Allah ya ƙarawa zamaninka tsayi, ya kare ka ko a gida ko dawa ayi haƙuri ina ƙara bada haƙuri namijin mazaje" Ba ƙaramin fasa masa kai kalamanta suka yi ba, duk da ba yau aka fara yi masa kirari ba, amma sai ya ji nata ya zama na musamman, har cikin kansa ya ji kirarin. Amma kamar wani basaraken zaki, haka yayi shiru ya cigaba da kaɗa ƙafa. "To in dafa ruwan wanka na kai toilet ɗin tsakar gida? Na san an gaji da yawa yau. Ya kalleta ya ce "Ba na so" Ta sakar masa wani ƙasaitaccen murmushi ta ce "Ai na ce ayi haƙuri, manya ba sa fushi fa" ta yi maganar cikin shagwaɓa. A taƙaice ya ce "Kai mini" Bayan yayi wanka, suka zauna a falo, suka ci abincin dare, dama tun a hanya ta sayo wa magenta kifi, ta nutsu tana bashi, tana yi wa master hira. Kasancewar ɗakunan an yi sabuwar plasta, ya sanya suka kwana a falo, sai da ya tabattar ta yi bacci, sannan ya fice tsakar gida yayi shaye-shayensa. Gaba ɗaya washegari jauhar a gidan mai ɗinki ta wuni, ta tayata aikin ɗinki, saboda gidanta su Al'amin suna aiki, hatta ƙofar gidan sai da aka yi wa plasta, gyara ko yaya yake kyau ne da shi, sai ga gida yayi kyau sosai da sosai. *** Yau ɗaya ga azumi, ranar jauhar tana da exams, Al'amin ya ce ta zo ta hau babur ɗin sa ya kaita, babu abun da ta tsana irin yadda yake yawo da babur ɗin babu salansa, ga babur ɗin kamar na 'yan gwangwani,saman babur ɗin nan duk a ragargaje, kana kallon wayoyin da aka yi wearing ɗin nan da su. Amma dan kar ta watsa masa ƙasa a ido, haka ya karkato babur ɗin, ta rirriƙe shi ta hau, suka tafi. Ko da ta dawo a gida ta tarar da shi, duk idonsa yayi ja, wanda idan ba da ƙwaƙwƙwaran dalili ba, ba za ka ganshi a gidan ba. Ta kalleshi ta ce "Master na dawo" Ya ɗaga mata hannu kawai. Ta shiga ta canza uniform, ta dawo yana kwance yayi wujiga-wujiga. Ta fito ta shiga kitchen, dan ta ɗora musu abun buɗa baki da wuri. "Master wai duk azumin ne, ko magana ta gagara" yayi mata shiru. Kawai ta hau dariya "Wallahi master ranar da babu abinci ban san yaya zaka yi ba, wato ba ka ko azumin nafila, yau ɗaya duk ka fita hayyacinka har haka?" Hararta yayi, yayi mata banza. Ta din ga yi masa dariya, ƙarshe ya koma tsakar gida ya shimfiɗa tabarma, yayi shame-shame kamar gawar sababi. Ko da aka sha ruwa, ba yadda ba ta yi da shi ya tafi masallaci ba, ya ƙi ya shanye lemo jug guda, da uban ruwa kamar amale, kuma ya fara da cin shinkafa, maimakon ya fara da abu mai ɗumi yaƙi. Ta ce "Ohh ni matar master, ya Allah kar ka hanamu abun da zamu ci a kowane hali, ranar da babu abinci akwai matsala master magana ma ta gagara yau azumi ɗaya kamar zaka rasu?" Yayi mata shiru yaƙi kulata. A ɗan tarin da take yi, da kuɗin da ya bata daf da azumi, tayi musu sayyayar kayan tea saboda tanadin azumi. Sai da aka yi azumi biyar, sannan Al'amin yake iya fita idan yana azumi, ya je ya ɗan yi neman kuɗinsa, gefe ga black market ɗin su ta sayar da kayan maye. Yau ya dawo da la'asar ya sheme a falo, sai sauke numfashi yake yi. Ta kalleshi tana dariya, ya kalleta ya ce "Ki ka sake ki ka yi magana ni da ke ne". Jauhar ta ce "A'a ni ban ce komai ba" tayi maganar tana cigaba da dariya. Tana ta aikinta an kusa shan ruwa ya ce "Anya kina azumin nan kuwa?" Ta ce "Ina yi mana" "Gani nayi yau sha bakwai ga wata, ba kya azumi" Ta kalleshi ta ce "To meye da sha bakwai ga watan?" Al'amin ya ce "Period ki ke yi, dan banaba kya azumi" zaro ido tayi cikin mamaki, yaya aka yi ya san tana period, cikin jin kunya, ta ce "Ni ba abun da nake yi, ba wanann date ɗin bane" Kawai ya gyaɗa kai, ya ce "Ai da ki ka gama cin ƙosan a kitchen ki ka cika cikinki, ba ki goge bakinki ba, kuma lemon da ki ka sha ma cup ɗaya kin sha naki, tun da ba azumi ki ke yi ba, sai iya yi mini dariya" ai kamar ƙasa ta tsage ta nutse, ba ta sanin ya ake yi, yake sanin ta aikata wasu abubuwan ta hau goge baki ta ce "Sa ido ba kyau, azumi ka ke yi kar ka zobe ladanka, ko a kwashe ladan naka a bani" Yayi murmushi bai ce komai ba. A wurin shan ruwa faɗa suka yi ta yi, wai ba zata cika kofi da kunu ba, ba tayi azumi ba, kamar sako da sakuwa. "Wai master, dan ban yi azumi ba ai ni na girka, sai ka barbaɗawa duniya ban yi azumi ba? Haba master" Ya ce "Eh ai ba yi ki ka yi ba, dan haka nawa sai ya fi naki yawa, ƙara mini" Ta tura baki ta ce "Aikuwa da gobe in Allah ya kaimu sai dai ka karɓo kunun sadaka, da ƙosai ka ci, ba zan yi girki ba, tun da ni ba na azumi, ko ka girka abunka". Ya ce "Eh dan dai girki, ba wuya zan iya, ƙosan nan ma rago shi nan, gandiya ƙatuwa da ke ba kya azumi" "Bani da lafiya ne" haka suka yi shan ruwan, ya din ga jin kamar bai taɓa shan ruwa da nustuwa irin wannan ba. Ita kanta tsokanar da yake yi mata daɗi take ji, bayan sallar isha'i ya zauna a falo, ya ɗauka zata yi masa surutun da ta saba, sai dai hankalinta ba ya kansa, yana kan magenta da take cewa boti, tana bashi abinci tana shafa shi, haushi ya ishe shi, shi gashi ba iya hirar yayi ba, balle shi ya fara, kawai ya tashi ya tafi ɗakinsa. Bayansa ta bi da kallo kawai ta yi murmushi ta ce "Master kenan, hukuma sai da rarrashi". Bakwai ga watan azumi ya kama ranar da za su bi Indabo campaign, tun dare ya haɗa yaransa da wurin da za su haɗu su tafi. Da sassafe bayan Jauhar ta tashe shi yayi sahur, ta idar da sallar asuba ta kwanta bacci, ya silale ya fice. Wunin ranar ba ta ganshi ba, ba ta damu ba sai da ta ga an kusa shan ruwa, ta din ga kiran wayarsa, amma ba ta shiga, sai hankalinta ya fara tashi, dan ta san duk in da ya je da an kusa shan ruwa yake tahowa gida. Al'amin kuwa bayan sun dawo daga campaign, an yi sare-sare sun yi shaye-shaye, an yi wa indabo aikinsa yadda yakamata, Al'amin ya sallammi yaransa, shi kuma Indabo ya ce ya bishi gida, da shi da wasu 'yan jami'iyya su sha ruwa a gidansa, ya sanya an shirya abun shan ruwa. Al'amin ya ce sai dai su tafi tare da walid. Ƙaton falo ne na musamman, mai ɗauke da haɗaɗɗem dining, kayan abinci aka kawo, na ƙasaita aka din ga jerewa a kan dining ɗin nan, cikin fulasai na alfarma. Walid ya ce "Mu na cin albarkacinka mai zamani, wannan sabga haka?" Al'amin ya bari, aka gama jere abinci, ana ta rawar jiki a fara ci ayi buɗe baki, ya tashi, ya bubbuɗe fulasan. Wani irin farfesu aka yi na kajin gidan gona, ƙosassu, ga flask ɗin dankali dana ƙwai abincin ma har da na almubazzaranci. Al'amin ya ja flask ɗin kaji, ya janyo na dankali, ya haɗe kan kayan shayi madarar gwangwani da milo, ya kalli Walid ya ce "Dafe mini wannan mu ɓace". Indabo ya ce "Ina zaka tafi kuma, za a ci abinci?" "Gida" ya bashi amsa. "To kuma na ga kana harhaɗe kan kwanukan abincin, ya zaka yi da su ga mutane za su ci?" Kai tsaye ya ce " 'yar madara zan kaiwa" "A'a ya mage zata yi da wannan uban abinci haka?" Walid ya ce "Ba mage ba ce, madam za a kaiwa" Indabo ya ce "Haba mai zamani, sai ka ce a ɗibar mata, amma yaya za ayi mutane na zaune abincin mutum sha biyu duk ka kwashe rabi?". "Ba zai yiwu da ni da na saka rayuwata a hatsari, da wanda ku ka tsaya a cikin rumfa hankali kwance, ka yi mana sallama iri ɗaya ba, ai kana da kuɗi a dafa musu wani. Ka san son zuciya ba halina bane, a baya ban yi ba ba zan fara yanzu ba. Ba zan ci wannan abincin ita ba ta ci ba, kuma ai ga wasu nau'in abincin nan ku ci. Walid ɗaukko kwandon kayan marmarin nan ma" Indabo ya ce "To fulasan fa? Ka tsaya sai a juye maka a leda, na madam ne wannan" "Madam ba ta fi madam ba, sadaki bai fi sadaki ba. Ina fatan ka fahimci lissafin? kuma kuna da kuɗin sayen wasu, ko ba yanzu ba idan kun ci zaɓe zaku samu, dan haka har fulasan mun cinye" Indabo yana ji yana gani, Al'amin ya yarfa shi a gaban jama'a, suka kwashe abinci suka tafi. Jauhar ban da ruwa babu abun da ta sha, har bayan sallar isha'i sai yawo take yi a cikin unguwar tana nemansa, hankalinta a tashe. Ta gaji ta dawo gida da nufin ta kira Walid. Kawai ta dawo ta tarar da shi. "Master ina ka tafi, hankalina ya tashi tun safe rabonka da gida, ba ka gaya mini ina zaka je ba, gaba ɗaya tun da aka sha ruwa na kasa cin komai, ban san ina ka ke ba". "To kukan zaki yi?" "Baka gaya mini ina zaka je ba, hankalina gaba ɗaya ya ƙi kwanciya haba master dan Allah" "Ohh murya kamar tsuntsuwa, yenyenyen, ki din ga buɗe baki ki yi magana sosai" kawai tayi shiru cike da takaici, idonta kawai ya kalla, ya san hankalinta a tashe yake. Ƙeyata ya tura, zuwa ɗakinsa kawai ta tarar da jeren kwanuka, haɗaɗɗun fulasai, da uban kayan marmari. Tayi saroro tana kallon kayan. "Zo ki zuba mana mu ci, ba kayan wani bane, mun je campaign ne muka dawo aka shirya shan ruwa, na ce a gida zan ci na taho da shi". A ɗan tsorace ta ce "Master duk wannan kuma?" "Eh kwaso kwanuka" Iya kajin sai da suka tsorata ta, dan sun kusa goma, fulasai ne na alfarmar gaske. Ta ce "Ai ba zamu iya cinyewa ba". "Gasu nan dai, ki yi abun da ya dace". Duk son Jauhar da nama, sai da ya isheta, ta bawa maƙwabta, ta zuba wani ya kira guduma a waya, ya ce masa ya zo ya karɓa. Hatta magenta, sai da ya ƙoshi da ciye-ciye. Haka kurum ya din ga jin annashuwa a ransa, ganin ta ci ta ƙoshi, har abun ya gundureta. Bayan jera masa godiya da ta gama yi, kamar yadda ta saba, tare da addu'oi, ta ce "Master Alfarma zan nema a wurinka dan Allah" "Ina jinki" Ta saka hannu ta karɓi wayarsa ta ce "Dan Allah kar ka ce mini a'a, ko ba zaka yi ba". "To kar ki tambayi abun da ba zan iya ba". "Zaka iya mai babban suna, kaga naman nan yayi mana yawa, duk da an babbayar dan Allah sonake na ƙara gyara shi, ayi miya gobe in Allah ya kaimu, mu je yi wa su baba sannu da shan ruwa" A take ya tsuke fuska, ya ƙi magana. "Dan Allah Master, na neman albarka mu je mu gaishe su" "Wai ke wace iri ce ne? Tun da muka yi aure, bayan su hajiya, kin ga wani ya zo gidan nan daga ɓangarena? Ko Abbun kin ga ya zo? Dama maraba suke nema da ni, har gara mahaifinki ma ya zo" Jauhar ta ce "Kar ka ce haka, dama ba su yakamata su zo ba, mu yakamata mu je, ai su iyaye ba a fushi da su, kai fa ka yi wa wani faɗa a kan haka, bai kamata kai ace ka aikata haka ba, dan Allah ka yarda mu je" An kai ruwa rana sosai tsakaninta da shi, kafin ya amince. Washegari suka shirya, bayan azahar suka fara zuwa gidan su Al'amin. Suka fara zuwa gidan su Al'amin, suka yi sa'a Abbu yana nan, sai dai rahila tayi mamakin ganin Al'amin, yayi wani shar da shi, sai ƙamshin turare yake yi kayansa sun sha guga. Ashe Abbu zuwansa gidan su biyu, ba ya samun kowa, a gidan, gashi Al'amin ya wanke ƙafarsa ya daina zuwa gidan. Abbu baki ya kasa rufuwa, mamaki yake ganin Al'amin, a nutse da shi ya sako 'yar matarsa a gaba gwanin sha'awa, sai dai sai cika yake yi yana batsewa yana wani basarwa. Dan tun da suka gaisa da Abbu, bai sake cewa komai ba, jauhar ce take bashi amsa idan yayi magana. Rahila ma sai zuba take ta ce "Ikon Allah, anya ba a canzo wani Aminun ba, kun yi kyau abunku kun ƙara ƙiba, an ce kin yi rashin lafiya kwanaki, To na san dai ba zai wuce laulayi ba, Allah ya raba lafiya" Al'amin ya ce "Amin, tashi mu tafi rana tana yi" kawai ta girgiza kai jin Al'amin ya amsa, idan ma haka ne ai kamata yayi, yayi shiru kawai. Rahila ta sake cewa "To sai ayi ta kula da ita, ka san masu ciki sai ana lallaɓa su, ban da hantara da abun da zai ɓata mata rai, kuma ba zama zaka yi ba, ciki tun yana ƙarami ake fara sayayyar kayan jariri". Jauhar ta ajiye food flask, da leda ta ce "Mama ga wannan, kwa yi buɗa baki, a saka mu a addu'a" Abbu ya ce "Masha Allah, addu'a kullum cikin yin ta ake, Allah ya yi albarka" Rahila ta ce "Iyee har da su suga da kayan marmari?" Ta buɗe fulas ta ce "Abbu kaza ce fa a ciki, ikon Allah sana'a ka samu ne haka? Ko kuma haryanzu miyagun ƙwayoyi ka ke sayarwa, gara mutum ya san halaccin abun da zai ci". Al'amin ya kalli jauhar, irin kallon kin ga abun da nake gudu ko?. Ya ce "Ubana na zo gani, kuma banda 'yar madara ta matsa, da sai dai na je ƙofar masallaci, idan ya fito na ganshi kamar yadda na saba, dan haka ba sai kin san sahihanci da halaccin cin sa ba, tun da bani da alaƙa da ke" ya tashi ya danƙi hannun jauhar a gaban su. Abbu ya ce "Aminullahi tsaya mana"ya tsaya cak yana huci, jauhar sai ƙoƙarin zame hannunta take yi daga nasa, saboda kunya. Abbu ya ce "Allah ya saka da alkhairi, ya yi albarka. 'ya ta Allah ya saka miki da alkhairi, yayi muku albarka gaba ɗaya" Ta ce "Amin Abbu, a sha ruwa lafiya " A zatonta, zai ta yi mata masifa, sai dai ta ji bai ce mata komai ba, ya wuce da ita unguwar su, ya kaita har ƙofar gida. "Ki yi sauri ki fito mu tafi, mu koma gida" Ta ce "To* Ta sauka daga babur ɗin ta shiga gidan, suka gaggaisa, sai dai baba baya nan, ta ce "Dama ɗan abun sannu da shan ruwa na kawo masa, sauri nake yi na bar shi a waje, kar ya gaji da jirana" Anty Zakiyya ta ce "Lallai jauhar, shi mijin naki ya fi ƙarfin ya shigo ya gaida mu kenan?" "A'a ba haka bane Anty, kin san ba ya jituwa da 'yan unguwar nan, bana son wani abu ya faru ne" Mama ta ce "Haryanzu bai shiryun ba kenan? Sai labari muka ji wai ya fito ai, Jauhar wannan naman kajin, shi ya saya ko ke?" Ta ce "Shi ne" Suryaya ta ce "To a dai yi a hankali, Allah ya sa ba na sata bane ba". Jauhar ta ce "Allah ya tsare shi, Al'amin ba ya sata". Anty Zakiyya ta ce "Wato Jauhar ba zaki yi mana Allah ya sanya alkhairi ba ko, ko kishi ki ke yi?" Cikin rashin fahimta jauhar ta ce "Anty na me?" "Alhaji mu'azzam ya dawo, tun da kin yi aure yanzu hafsa zai aura, ya bayar da miliyan biyu tayi lefe, dubu ɗari biyar kuma kuɗin aure!" Ayshercool 08081012143. 34 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Abunka da zuciya, dumm haka ƙirjin Jauhar ya buga, da ƙarfin gaske, take wani abu da ba ta san menene ba ya taso mata. A ranta ta ce "Saboda haka dama ku ka aura mini Al'amin, dan rusa aurena da Alhaji mu'zzam?" 'kul jauhar, Al'amin zaɓin Allah ne a gare ki, babu wanda yake da ikon canzawa wani ƙaddararsa, dama haka Allah ya tsara miki' Cikin sauri ta ce "Ahh haba, amma ba a gaya mini ba, ga shi muna waya, ina yi muku magana ta what's app, Anty ke ma ina da lambarki, amma ba a gaya mini, ko dan kar in haɗa lefen na zo na ɗauki kayan kwalliya ne ya sa ba a gaya mini ba?" Anty Zakiyya ta ce "A'a kar a gaya miki ki ji wani abu a ranki ne, dama Allah bai ƙaddara mijinki bane" Jauhar ta ce "Haka ne, mijin wata baya auren matar wani, idan an gama haɗawa ni dai zan zo a bani kayan kwalliya". Surayya ta ce "Au, ashe fa ba ayi miki lefe ba ke ko?" Jauhar ta girgiza kai ta ce "A'a kin manta an yi mini sayayyar kaya?" "Duk da haka wannan ai ba lefe bane ba" Wayar jauhar ta fara ringing, ta cirota daga jakarta ta ce "Master" "Fito mu tafi" "To gani nan" "Bari na tashi yana jirana, idan an saka lokaci sai a gaya mini" Hafsa ta ce "An saka bayan salla da sati uku ne" "To Allah ya sa zamu gani, a gaishe mini da baba, sai kuma Allah ya kaimu salla, Anty walida ku kuma na gaji da roƙonku ku zo gidana, ko sau ɗaya babu wanda ya taɓa yi mini kara ya zo". Hafsa ta ce "Ke fa babu wanda zaki gani a gidanki, muna yayyenki zamu din ga zuwa gidanki, ko so ki ke mu zo mijinki yayi mana illa?" "Haba dai, ba fa mahaukaci ba ne, da zai yi muku illa, da ban kawo yanzu tare da shi ba, sai anjimanku" Zuba mata ido yayi, har ta ƙaraso, sai dai ya lura da jikinta a sanyaye yake, bai ce mata uffan ba, ya kunna babur ɗin, ya karkata mata ta riƙe shi ta hau suka tafi. Sai yanzu ta ƙara gane dalilin yin amfani da yi mata sharri, wurin aura mata Al'amin, ba wai tana baƙin ciki da auren hafsa bane ba, ta san haka Allah ya ƙaddara kawai mamakin tsananin ƙin da suke yi mata take yi, ta san ko da kuɗi ba za su yadda su aurawa 'ya'yan su mutum irin Al'amin ba, saboda kar ta huta shiyasa suka yi mata wannan muguntar. Kallon bayan Al'amin take yi, a ranta ta ce "Kai Allah ya zaɓa mini, kuma in sha Allah sai na yi kyakywar rayuwar aure da kai master'. Da haka suka ƙaraso gida, sai dai yana ankare da yadda walwalarta ta gushe, take komai jiki a sanyaye babu kuzari. Ɗan muzurunta na ta kewayata, yana yi mata ɗan kuka, amma ta kasa kula shi, wanda da tana cikin walwala da tuni ta ɗauke shi tana yi masa rawa, da ma shi ba shiri yake yi da muzurun ba, dan dana sanin kawo mata shi ma yake yi, saboda yadda take tsananin ba wa muzurun kulawa, kamar ya jefar da shi haka yake ji wasu lokutan. Ya zuba mata ido, tana ta yi wa wani mayafi ado da beads, na kayan sallar mutane da take ta yi, sai dai a saɓule take  aikin. Muzurun ma ya gaji, ya koma gefe ya kwanta, saboda ta kasa kula shi. Har aka sha ruwa, ko surutun yau ba ta iya yi, abincin ma cakalarsa kawai take yi, ta kasa ci ta ajiye ta tashi tayar da sallar taraweeh. Ta cigaba da aikin beads. "Ssss, Ji mana" ta ɗaga kai ta kalleshi. "Zo mana"ta ce "To" ta yinƙura ta tashi, ta ƙaraso gaban sa, tana ƙoƙarin zama a ƙasa, ya nuna mata kusa da shi, ta zauna tare da sunkuyar da kanta. "Kin ga muna zamanzamanmu, ki ka kwashe mu, muka je wurin mutanen nan, gashi kin je an yi miki wani abun kin kasa sukuni, shiyasa tun farko na ce kar mu je, ki ka dage, kin dawo kin kasa nutsuwa, me aka yi miki?" Ta girgiza masa kai ta ce "Bakomai" Ya ce "Bana tambaya sau biyu" "Ka yi haƙuri dan Allah, babu komai, zuwa da safe zan wartsake in sha Allah". "Ba ki da juriya, kin fiye rauni, da wuri ake ganin gazawar ki, ki ƙara ƙoƙarin zama jaruma, ko dai ayi miki ki shanye ko shirya ramuwar gayya sama da abun da aka yi miki. Ki ajiye wannan abun da ki ke yi, ki tafi ki je ki kwanta" Ta jinjina masa kai ta ce "To master, na gode sosai" ta tashi jiki a sanyaye ta tafi ta kwanta. Sai dai bacci ya gagari idonta, ta din ga tunanin, meke damunta kishi ne ko hassada. Sai dai ta tabattar wa da kanta ba kishi bane ba, saboda ta riga ta zama matar wani, ko ba komai a yadda yake ɗin nan, ta fara appreciating yanayin zaman na su yanz saɓanin da, dan haka tana matar wani ba zata yi kishi a kan wani ba. Hakazalika ba hassada ba ce ba, ba ta ji ta damu dan hafsa zata shiga cikin daular da, da ita ce zata shiga, ta san wannan nufin Allah ne, kawai tana jinjina yadda suka shiga suka fita, suka aura mata Al'amin dan kawai kar ta auri Alhaji mu'azzam. Wannan gillin ɗabi'a ce ga zuciya, da duk yadda ɗan adam ya kai ga dannewa sai yayi tasiri, ta din ga istigfari da roƙon Allah ya sanyaya mata ranta, ta manta ta fuskanci Rayuwarta. Yanayin yadda Al'amin ya fara nuna damuwarsa a kanta, ya ke sanya wa ta ji tabbaci da ƙwarin gwiwar cewa wataran za ta ji daɗinsa, tun da dai babu duka ko zagi a tsakanin su, shaye-shayen sa da nema rigimarsa ne babbar matsalarta, gashi yanzu cefane ma yana yi ko ba kullum ba. A cikin kwanakin da ta dage da addu'a, sai ta fara jin sassauci ta fara mantawa, ta cigaba da mayar da hankali a kan sana'arta, da yi musu Addu'a babu dare babu rana. Al'amin ya fara rage yin shaye-shaye a gabanta, sai ta yi bacci, sai ya fita tsakar gida, ko ƙofar gida yayi, duk da wasu lokutan idan ta shiga ta tarar da shi yana yi, mazewa yake yi ya haɗe rai ya cigaba da shan abun sa, amma sosai yake rage abun da zai yi, wanda zai sanya ta shiga damuwa. Ya mayar da ita asibiti, likita ya tabattar da jininta ya sauka, kuma ya dakatar da ita daga shan magani, na wani ɗan lokaci. Saura sati guda salla, gidan jauhar mutane ne kawai ke shiga suna fita, masu mayafai, masu ɗinkuna da zata yi wa stone work, masu kitso da lalle, a haka kuma tana kasa kayanta, na shirin dutse, sarƙa abun hannu, jigida, ga kayan lemo, masu zuwa kitso suna yi mata ciniki. Ta zama very busy, idan yamma ta gabato, ga aikin abinci, sai dai garin Allah yana wayewa, ya fice ya bar gidan, saboda mutane. Sai dai ana shan ruwa take sallamar kowa, ta ce sai gobe, za ta kula da mijinta. Yana falo a zaune, ya gama shan ruwa ya kasa tashi, wata mata tayi sallama, tayi ta yi wa jauhar magiya, wai tana son ta turo yaran, ta wanke musu kai, tayi musu kitso, kowace yarinya ɗari da hamsin, su huɗu. Jauhar ta ce "Haba Maman Nana, ki bani ɗari bibbiyu mana, ga wanke musu kai, ga kitso?" "Taimakawa zaki yi jauhar, idan ki na son gobe mu kawo miki coustomers, kin san yadda garin yake, ubansu bai bani ko sisi ba, ni nake wahalata dan yaran su fito fes, ko hankici bai yi mana ba" Jauhar ta ce "To shikenan, bari na sallami master, gobe in Allah ya kaimu akwai mutane sosai, turo su yanzu a wanke musu kan, in dafa ruwa a heater tun da da wuta, gobe in Allah ya kaimu da sassafe sai ayi kitson" "Ke, na hana kitson, kwashi yaranki ki tafi wani wurin ayi miki" ta ji muryarsa a ƙofar falo. Jauhar ta ce "Master meyasa?". "Na hana kitson, duk wannan wahalar da ki ke wuni kina yi a ɗari da hamsin? Dama wuni ki ke wahalar banza, saboda aikin yi yayi miki ƙaranci? Get out malama kwashe yaranki ki fita, iyayen son banza". Kamar jauhar ta yi kuka ta ce "Master dan Allah... "Shhh" yayi maganar yana ɗora yatsansa a kan laɓɓansa. Matar ta fita ta kalleshi kamar za ta yi kuka ya ce "Na ga aiki ne yayi miki ƙaranci, mu je ina da aikin da zan baki ni, ki zauna ki wuni kina wahala, a ɗari da hamsin, ina zaki kai kuɗi ne wai? Duk kin rame saboda kin saka azabar son kuɗi a ranki" Yayi maganar yana kallon ta, tana tsaye tana tura baki. Ya fizgota gabansa ya ce ya kai hannunsa wuyanta ya ce "Wannan ƙashin na wuya da ki na shi? Duk kin yi wuri-wuri ga azumi ga wahala" da sauri ta ɗan kama jikinta, saboda unexpected ya saka hannunsa a wuyanta. Maimakon ya sauke hannunsa, sai ya miƙar da hannunsa zuwa kan maƙogwaronta, ya fito da dogon harshen sa har wurin haɓarsa, ya lanƙwasa shi, sannan ya mayar cikin bakinsa ya ce "Na ga kina motsa baki, me zaki ce?" Jauhar ta ce "Ai shikenan ka korar mini coustomer, kuma ka shaƙeni zaka kasheni ka huta. Kuma sai ka biyani kuɗin wanda ka korar mini, ɗari shida" "Bana son ganin wannan ƙashin, kwana uku kawai na baki ya koma" yayi maganar yana sake shafa wuyanta. Riƙe hannunsa tayi, tana kallon idonsa, da abun da yake yi matan ko a jikinsa. Ɗan muzurunta ne, ya yo tsalle yana yakushin ƙafar Al'amin, saboda riƙe wuyan jauhar da ya yi, yana kuka. Al'amin ya kalli muzurun, yayi cilli da shi, ya ce "Na kusa mayar da abun nan in da na ɗauko shi, ya fiye zaƙewa, zo ki yi mini aikina" Ta biyo shi tana mitar ya korar mata coustomer's , ya nuna mata kujera 3seater ya ce ta zauna. Ta nemi wuri ta zauna, ya kwanta ya miƙe ƙafafuwan sa a kan cinyarta ya kaɗa mata yatsunsa, alamar tayi masa tausa. Ta ji haushin yi mata asarar ɗari shidan da yayi, shi kuwa ko a jikinsa, sai dai ƙasan zuciyarta mamaki take yi, ashe yana kallonta har haka da ya gane ta rame. Iya ƙarfinta ta saka tana jan yatsun ƙafarsa, tana son yayi magana, amma ko a jikinsa. Tun tana yi da marmari, har ta fara gajiya, dama gashi wuni tayi aiki, tun tsakiyar azumi rabonta da baccin kirki. A take ta fara gyangyaɗi, bacci mai ɗan nauyi ya yi gaba da ita, kamar a mafarki ta ji abu yana taɓa cikinta, ta buɗe idonta ta ga menene, babban yatsansa ya saka yana taɓa cikinta. Da sauri ta ɗame cikinta, ta kalle shi, ya rufe idonsa kamar mai bacci. Ta riƙe ƙafarsa, ta sake kallonsa, amma ya saka ɗayar ya cigaba. Ta saka duka hannunta biyu, ta rirriƙe ƙafafunsa, tana ajiyar zuciya kamar mara gaskiya. A hankali ya buɗe idonsa, yana kallonta, ta sake ɗaga kai ta kalleshi, suka haɗa ido, tayi saurin kawar da kanta. "Dambe zamu yi ne ki ka rirriƙe mini ƙafa? Tausa fa na ce ki yi mini". Kamar ta yi kuka ta ce "Na gaji bacci nake ji" "Eh da aikin banzanki ne, ba zaki gaji ba ai, kin ga yanzu kya samu lada sama da ɗari shidan da ki ke yi mini ƙunƙuni a kanta" A shagwaɓe ta ce "Ni ba ƙunƙuni nake yi ba fa, ka yi haƙuri to" ya janye ƙafafuwan sa daga kan cinyarta, ta tashi da sauri, muzurunta ya bi bayanta, ta saka hannu ta ɗauke shi ta nufi ɗaki. Baba ya ji daɗin abun da ya tarar jauhar ta kai masa, ya din ga murna da sanya mata albarka, tare da yi mata addu'a iri-iri. Ganin hankalin Jauhar yana kan 'yan kuɗaɗen da take samu, na sana'ointa, ya sanya ya ƙyaleta, baya son yawan takura mata. A goman ƙarshen nan, haka ta din ga damunsa, a kan yawaita ibada, dan azumin kawai yake yi, ba sauran ibadu. Da ƙyar take saka shi yayi salla cikin dare ko raka'a biyu ce. Dama idan aka sha ruwa, ya ƙoshi sai ya je dabar su, sun yi shaye-shaye tukuna ya dawo gida. Ana jibi salla, ta saka shi a gaba da naci, da magiya, su je ayi masa aski saboda gabatowar bikin salla ƙarama. Ya ce na za shi ba, ƙarshe ita ta zauna, ta wanke masa kan, ta rage masa sumar da almakashi, tayi masa gyaran fuska da shaver, tamkar ɗa da uwa. Ana gobe salla, ta yi masa list dai-dai na talaka, ta ce ya sayo, za ta yi abincin salla, dan abubuwa da dama idan ba ta ce masa yayi ba, ba zai yi ba, idan kuwa ta ce ya sayo zai sayo, idan ba shi da hali kuma zai gaya mata ba yanzu ba. Da sassafe ƙarfe bakwai, ta shigo ɗakinsa da mp ɗin ta, an sako kabarbari da ake yi yayin tafiya idi, tana maimaitawa. *Allahu Akbar, Allahu Akbar la'ilahaillala* *Allahu Akbar, Allahu Akbar walillahil hamd* *Allahu Akbar kabiran* *Walhamdilillahi kathiran* *Wa subhanallah bukratan wa asila* "Master, kar mu makara sallar idi fa, ka tashi" ya motsa a hankali yana yamutsa fuska. Ta miƙa masa hannu ta ce "Barka da salla? Ina fatan ka yi sallar idi lafiya" Yayi miƙa tare da hamma, ta ce "A'uzibillah, Alhamdilillahilazi ahyana, ba'ada ma amanatana wa ilaihil nushur. Ga ruwa mai zafi can, ka zo ka karya mu shirya" "Sai na karya tukuna" "To taso ka yi brush, ko sai na ɗauke ka ne, sai ƙara maƙalewa ka ke yi a katifa" Kukan ɗan muzurun nan ne ya sanya Al'amin shi tashi zaune ba shiri, ya biyo jauhar yana yi mata ɗan kuka. Ta kalli muzurun ta ce "Sweetheart, mu je na baka abinci" Al'amin ya tashi ya bar ta da muzurunta, saboda zaƙewar muzurun ta fara yawa a kan matarsa. Ya fito daga wanka, ta shigo ɗakin da wata leda, ta saka dogon hijjabi light blue, sai zuba ƙamshi take. "Master yi sauri zamu makara" Ya shafa mai, ta buɗe ledar ta fito da ɗinkakkiyar shadda light blue, da hula, ga agogo sai takalmi soso na ta da nasa, iri ɗaya na ta na mata na sa kuma na maza. Turus yayi yana kallonta, cikin tsananin mamaki. "Ungo saka, bari na je na rufe ɗakina kan ka gama" Kamar soko ya kasa karɓar kayan. "Ko ba ka so ne?" Tayi maganar a sanyaye. "A ina ki ka samo wannan kayan?" Ta ce "Dama ana samo kaya ne? Neman kuɗin da ka ke cewa na saka a gaba ne, ka san wata nayi ina yi mana tarin nan? Hmm saka kayanka ina zuwa bari na ɗaukko wayata da darduma" ta ajiye masa ta fice. Kallon kayan ya din ga yi yana jujjuya su, har da aiki a jikin kayan, shi bai yi mata kayan salla ba tayi masa?. Ya saka wandon, ya tsaya yayi shiru yana kallon rigar, har ta dawo ɗakin. "Master saka mana" ta karɓi rigar tana ɓalle botiran jiki, ya karɓa yana sakawa ta ce "Alhamdilillahilazi kasani haza saub, waraƙatani min gairi haulin minni wala ƙuwwa" Ta saka masa hula, ta saka masa lence ɗin hannun rigar, ta ɗaura masa agogo, tare da saka masa farin glass na maza. Tayi wani irin murmushi ta ce "Tubli wa yuklifllahu ta'ala. Wallahi kana da kyau master, ka ga yadda ka yi kyau kuwa? Subhanallah saka takalmin mu ke falo na yi maka hotuna" gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, ashe matan ma sunan suka tara? Wace irin mace ce jauhar. "Master ka yi dariya mana, sai hoton ya fi kyau" Ta gama yi masa hotunan, ta riƙo hannunsa, ita ma ta saka nata gilashin fari, suka fita sallar idi. Musulunci mai daɗi, al'ummar musulmi na ta ɓarkowa ta kowane angle zuwa masallacin idi. Shi rabonsa da zuwa sallar idi ma, har ya manta lokacin, amma yau albarkacin auren mace ta gari, ta saka shi a gaba har zuwa masallaci. Aka idar da sallar idi, suka haɗu a wani gate ɗin daban, bisa koyi ga sunna, jauhar ta bawa wata wayarta, ta ce dan Allah tayi mata hoton first eid with habinbi. Ta ɗauka zai ce baya so, bisa ga mamakinta, sai ta ga ya saka hannu, ya dafo kafaɗarta jikinsa, yana kallonta, ta saka hannu ta zagaya a ƙugunsa kasancewar da kaɗan ta wuce ƙugunsa, ta kalleshi ita ma tana murmushi. Hotunan sun yi kyau sosai, banda wanda ya yi wa Al'amin kyakkyawan sani, ba zai gane shi ba, sai ya zama very decent and calm. Har suka dawo gida, hannunta na cikin nasa, cike da shauƙi da nishaɗi. Ya karɓi mukulli ya buɗe musu gida suka shiga, jauhar baba ta fara kira, ta yi masa barka da salla, ya ce mata idan mijinta na da account, ta tura masa ya saka mata barka da salla. Ta kira yaya saifu ma, haka ta din ga bin family tana yi musu barka da salla. Ta kalli Al'amin ta miƙa masa wayarta ta ce "Saka mini lambar baba, mu yi masa barka da salla" "Bani da ita" ya bata amsa. Ta marairaice ta ce "Dan Allah master" Ya ce "Sai kuma ki yi" Haka ta haƙura ta tashi ta ƙyale shi, ta tafi ɗakinta, ya din ga kallon kayan jikinsa, yana sake jinjina ƙoƙari da ƙarfin hali irin na jauhar, wai shi ta yi wa kayan salla. A status ɗin ta, ta yi posting "Alhamdilillah first eid with my amazing Habibi, Allah ya ƙara wa zamaninka tsayi, ya maimaita mana" Surayya ce ta fara ganin status ɗin, ta din dariya tana nuna wa 'yan gidan, suka din ga cewa pretending ne, na lallai sai ta nuna wa mutane tana cikin kwanciyar hankali, sai dai suna tsaka da gulmar, ta sake saka hotonsu riƙe da dadduma a filin idi, wanda hakan ba ƙaramin girgiza su yayi ba da ba su mamaki. Master ya kai mintuna goma sha biyar yana zaune, ta fito sanye da leshinta da ta saka ranar ɗaurin aure, ta shafa powder da jambaki, ta saka kwalli, ta kwantar da gashin gaban kanta, da gel, ta yi ɗauri mai kyan gaske, gashi ta kaiwa Suwaiba tela ta gyara mata ɗinkin, dai-dai jikinta. Har ya tashi zai shiga ɗakinsa, ya waiwayo ya ganta ta fito, mp ce a hannunta, tana bin waƙar da aka saka, a cikin nishaɗin barka da salla. Cikin waƙar m sharif *Farin gani kai ne tauraro, ko a cikin samari, mai ji da ni ba ka yin ƙwauro ka sa na wuce gori, na ɗau takarda na riƙe biro, kai na saka a fari, kai zan ba dawakai, kowanne da silkai, matsayinka ya kai ba zan yi ma kishiya ba....... Da haka ta ƙaraso gabansa tana rawa, tana yi masa fari da ido. Tsayawa yayi yana kallonta yana murmushi, sai dai bai tsinke da lamarin na ta ba, sai da ta ƙaraso gabansa ta riƙe hannunsa wai sai ya yi rawa. Karo na farko da ya buɗe haƙoransa talatin da shida yayi dariya. "Ba dariya zaka yi ba, ka yi mini liƙi ko ka yi mini rawa" ya buɗe baki ya ce "You are not serious" "Am serious mana, rawa ko liƙi, biyani ɗari shida ta ma da ka korar mini coustomer's" ya saka hannu a aljihunsa ya ciro dubu biyu da ɗari uku ya ce "Suke nan nake da su, uwar son kuɗi" "Ungo dubu ɗaya, sauran bari na bayar da ayata a markaɗo mini, na haɗa da snacks da tuwon salla na raba. Ba ka ce ma na yi kyau ba, ka taɓa ganin mace da tayi kwalliya tayi kyau kamar yadda na yi yau?" Yayi murmushi ya ce "Ni da ba kallon mata nake yi ba, ya za ayi na sani, ni dai ba ki yi mini kyau ba, kamar babyn roba haka ki ka zama" yayi maganar yana matsa kumatunta. "Daga Angela zuwa 'yar madara, yanzu kuma babyn roba?" "Eh, irin na wasan nan ba" Jauhar ta ce "Kyau nayi maka ne" Ta fice tsakat gida, tabbas tayi kyau kam, tayi fresh farar fatarta ta karɓi baƙin leshin sosai da sosai, kwalliyar ta yi mata kyau. Tana tsakar gida, wasila ta shigo ta kawo mata tuwon salla, suka gaisa tare da yi wa juna barka da salla. Wasila ta ce "Jauhar iyayen soyayya, mu matan layin nan, tare muka haɗa kai muka tafi idi, a hanya muka hango ku, an maƙalƙale hannun master ana yashe baki, kai jauhar a ji tsoron Allah" Jauhar ta ce "Anty wasila kina saka mini ido wallahi, ki sa ka in ta jin kunya" "Ke ba wata kunya, riƙe abunki wallahi, abunku gwanin sha'awa, kafin lokacin ya wuce, ba kowane namiji ne yake jure ayi ta soyayya ba". Al'amin ne ya fito, Wasila tayi tsit dan ba ta san yana nan ba, ta gaishe shi ya amsa ciki-ciki. "Master ina zaka? Kunun aya ka san baya daɗewa" "Nura ne a waje ya kirani, ba nisa zan yi ba" Ta ce "Ok to" Daga jikin gate guduma ya ce "Antynmu barka da salla". Jauhar ta ce "Yauwwa malam nura, ina fatan ka je idi?" "Eh na je, na biyo mu gaisa sannan ki bani tuwon salla". Jauhar ta ce "Aikuwa ka samu, amma sai ka kai mini markaɗen aya, ka sayo ƙanƙara sai na haɗa maka da tuwon" Ya ce "Ba case matar babban yaya" Al'amin bai sani ba, har gidansu jauhar ta aika da abincin salla, guduma ne ya kai ya kai na gidan su ita ma. Ta zuba wa Al'amin, ya tafi da shi, tun da ya shiga wurin na su, Liti da sauran yaran suke bin sa da kallo. Liti ya ce "Maza, wannan shuɗiyar audugar ruwan sararin samaniya fa, waye ya sayeka cikinta?" "Ban sani ba" Walid ya ce "Abun a tambaya ne, ni fa tun da na sanka sau ɗaya na ga ka saka manyan kaya, ranar da aka zarga maka uku, ina nufin igiyar sunnar ma'aiki da bint laban ɗin ka, wato madam 'yar madara" Ya tsuke fuska ya ce "Mai laya" Walid ya ɗaga masa hannu ya ce "Tuba nake, na kiyaya wannan ma'adanar abincin fa?" Al'amin ya ajiye musu kwanuka, suka dirarwa abincin nan da ci babu ji babu gani. Baba kuwa yaya saifu ya aiko, aka kawo mata fulasanta, da kuɗi dubu goma, kasancewar ba ta tura account number da ya ce ba a matsayin barka da sallar ta. Da daddare da ya dawo, yana shigowa ta ji warin sigari, dan da alama ma a cake yake, bai kulata ba, ya tafi ɗakinsa ya baje a kan katifa, ta bi bayansa har cikin ɗakin, cikin matsananciyar damuwa ta ce "Haba master, shi ne ka je ka sha da yawa, kalli a yadda ka dawo fa, gaba ɗaya ka ɓata mini ɗan farincikin da na tsinci kaina a ciki yau" yayi shiru yana sauke numfashi. Ta ƙaras ta ce "Tashi a cire kayan to, sai ka saka wasu" "Get out" "Ai zan tafi amma...... "I said get out" yayi maganar cikin tsawa. Ta tashi a razane, ta bar masa ɗakin, cikin azumi dai Allah ya taimaketa ya ɗan nutsu, saboda baki a rufe yake, ba ya shaye-shaye sosai, yau da ga sallacewa ya koma ruwa. Saboda tsabar takaici, ko baccin kirki ba ta yi ba. Da safe kamar ba shi ba, ya tashi ya fito abun sa, ya sayo abun karyawa, sai share shi take yi, amma ya nuna ko a jikinsa. Kasancewarta mai matukar raunin zuciya, sai kuma ta sake. Suna karyawa, Hafsa ta kira ta a waya, jauhar ta ɗaga tayi mata sallama ta ce "Amarya ba kya laifi" "Mhmm, dama anko ne mama ta ce sai an nuna miki, shi 'yan gida za su yi da bikina, zan turo miki ta what's app lace ne dubu goma sha biyar sai atamfar kamu dubu tara, na san ba lallai ma ki yi" Jauhar ta yi murmushi ta ce "Anty hafsa kenan, aikam dai kun san mijina talaka ne, zan sako dai abun da Allah ya hore mini na zo, in sha Allah" "Dama na sani ai, mama ce ta takura a turo miki kar abun ya zama surutu, a ga kin fita daban. Allah ya sauwwaƙe tisya" "Ba tsiya ba ce anty hafsa, idan ruwanka bai isa alwala bane sai ka yi taimama Allah ya kaimu bikin lafiya" ba shi aka gaya wa ba, amma sai ya ji maganganun hafsan tamkar direct da shi take, wani irin haushi da takaici ya kama shi. Sai dai ya basar ya cigaba da karyawa abun sa. Ya kammala ci, ta tashi ta yi aikace-aikacenta, yau ma wata kwaliyyar ta yi da abun da Allah ya yassare mata. Ya ce "Babyn roba" Ba ta kalle shi ba ta ce "Saura ta rodi" "Zaki gama kumbure-kumburen naki ki sace" Ta share shi, tana shafa muzurunta d take cewa boti. "Ina magana ki ka share ni, kina wasa da wannan abun da nake dana sanin kawo shi?" "To me zan ce maka? Kawai ka je ka sha abun da ka sha, daga yi maka magana ka hantare ni" tayi maganar idonta na cika da hawaye, saboda takaici. Maimakon ya damu, sai yayi murmushi ya saka hannu ya matsa kumatunta a hankali ya ce "Abun wasa na, you are like a toy to me, wani abu mai ɗan bani nishaɗi wasu lokutan" Galala take bin sa da kallo, ita ce ma abun wasan. "Kin daɗe kina yi mini abubuwa, abun da ki ka yi mini jiya ya tsaya mini a rai, ki ka ɗinka sutura sukutum ki ka bani, Allah ya suturtaki ranar da bayi za su tsaya a gabansa babu sutura. Na gode Allah ya baki miji nagari" Da sauri ta sake kallonsa, sakamon abun da ya faɗa na Allah ya ba ta miji nagari. "I still mean it, haryanzu ina kan bakana na rabuwa da ke a duk lokacin da ya dace, kina takura mini da yawa" A fusace ta saka hannu, ta buge hannunsa da ya riƙe kumatunta, ta waiwaya tana kallon gefenta. Ya ce "Idan ki ka kuskura ki ka jefe ni, yau ni da ke ne" tashi ta yi tana kuka, ta nufi ɗakinta. Ayshercool 08081012143 35 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Ba ta ƙara kula shi ba wunin ranar, dama kuma ficewa yayi ya bar gidan, ta rasa sai zuwa yaushe Al'amin zai yadda ya karɓeta su yi rayuwa, kullum ba shi da magana, sai maganar da zata tayar mata da hankali na zai rabu da ita, gaba Al'amin yayi hannun riga da duk wani nau'i na  tausayi. Abun da zuciyarsa ta raya masa kawai yake yi, ko ya yi maka daɗi, ko akasin haka ba damuwarsa bane ba. 'yan yaran da suka din ga shigo mata yawon salla, su ne suka din ga ɗebe mata kewa da rage mata damuwa. Sai bayan sallar magariba sannan ta sake ganinsa, tun da ta yi masa sannu da zuwa, ta ajiye masa abinci, ta koma gefe ta na danna wayarta. Sai da ya ci ya ƙoshi, ya samu wuri a kusa da ita ya zauna, ya ce "Abun wasan, ya dai?" Ta ɗaga kai ta kalleshi ta sunkuyar, ta hau wasa da yastun ƙafarta. Hannunsa ya saka shi ma a yatsun ƙafarta yana tayata wasan da take yi da su. "Master" "Mmm" "Meyasa ka ke son lallai sai ka sake ni ne? Saboda ka ga bani da makoma ko? Ban taɓa burgeka, duk ƙoƙarin da nake yi, ba ka appreciating kullum cikin tsorata ni ka ke, kana gaya mini abun da zai ɗaga mini hankali, me nayi maka ne?" "Baki dace da ni ba, da salihin mutum nagari ki ka dace. Da zan iya samun mutum mai amana da zai riƙe ki, zan iya rabuwa da ke ya aura, you  have an innocent soul, that doesn't deserve someone like me, shiyasa nake yawan gaya miki haka. Ko jiya a fusace nake, na yi miki tsawa sai da ki ka yi kuka, ina ɗaukar hakkinki" "To ni na ce maka bana son zama da kai ne? Ina yi maka addu'a, wataran zaka daina ai ko?" Tayi maganar tana kallonsa. Yayi shiru bai yi magana ba, "Dan Allah ka yi magana, zamu iya rayuwa tare, irin damuwar mu ɗaya, matsalar iyalan da muka tashi a tsakanin su, ba sai mu zama familyn junanmu ba, mu rayu cikin aminci da walwala. Amma master meyasa ka ke shaye-shaye bayan ka san yana da illa ga lafiyarka? Yana saka aikata abubuwan da bai kamata ba, kayi faɗa da mutane a zubar maka da jini, ko ka zubarwa wani, har kisan kai fa yake saka". "Wa na kashe?" Ta ce "Ranar da na fara ganinka, a unguwarmu, gawar wani na ganka da ita ka soka masa wuƙa" Yayi murmushi, ya haɗiyi wani abu mai ɗacin gaske. "Ban taɓa kisan kai ba, ranar ce haɗuwarmu ta farko ko? Ban kashe kowa ba" Cikin damuwa ta ce "Amma wuƙa fa na gani a gefen cikinsa, kuma meyasa ka ke shaye-shaye?" "Bana son silly question, rabu da ni" ta gyaɗa kai kawai ta ƙyale shi. Ranar hawan salla kuwa,  Jauhar ba ta san me ake yi ba, Al'amin ya haɗa yaransa, da miyagun makamai, da sunan tsaro kar wasu daga wani wurin su zo su fake da kallon hawan salla, su kawo musu farmaki su cutar da wani. Sai dai sun yi ba ta kashi da wasu marasa jin sosai da sosai, ciki kuwa har da yaran madaki. Sai da 'yan sanda suka yi kame sosai da sosai, daga wurin hawan Al'amin bai koma gida ba, ya wuce cikin gari, saboda kar jauhar ta ganshi da makami, da jini. A cikin garin ma, sai da suka yi wata fitinar, aka yi sare-sare da faɗace-faɗace. Sai bayan kwana biyu, jauhar take jin labarin abun da ya faru a wurin hawa, ganin Al'amin lafiya ƙalau ya sanya ta kwantar da hankalinta, tare da bawa kanta yaƙinin cewar babu shi a rigimar. Kwana na huɗu, tana kitchen tana girki, tana shirin kaɗa miyar cin tuwo, maman halimatu ta shigo gidan a gigice. Jauhar ta ce "Maman halimatu lafiya kuwa?" "Ke kina nan baki san abun da yake faruwa ba?" Cikin rashin fahimta ta ce "A ina?" "Wani ɗan daba ne wai madaki, daga can unguwar ku ya zo unguwar nan wai neman mijinki, wai ya illata masa yara, sai tarwatsa mutane suke yi, suna sara kan mai uwa da wabi a guje na ƙaraso" Cikin tashin hankali ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" take kanta ya sara, jikinta ya hau rawa, ta ɗauki wayarta ta kira lambar sa, sai dai tayi ta ringing baya ɗagawa. Hijjabinta ta ɗauka, maman halimatu ta ce "Ina zaki? Saran mutane fa suke yi, duk wanda suka samu duka ko sara". Ai ba ta ko tsaya bata amsa ba, ta fita cikin matsanancin sauri da tashin hankali. Ba ta san in da za ta nufa ba, addu'a kawai take yi da roƙon Allah, Allah ya tsare mata mijinta. Mutane na guje-guje ita kuwa kutsawa take tana duba ina zata ganshi tana kuka. A wani layi ta hango shi, ya riƙe wani matashi, idon Al'amin kawai ta kalla ta san a buge yake, babu alamar mutunci a idonsa, idanun sun yi jawur sai gumi yake yi, yanayin sa ya tabattar mata da ya tafka ɓarna, kafin ta ƙarasa, ya fito da harshen sa waje, kamar yadda yake yi, idan ya ƙudirci aniyar yin wani abu, ya ɗaga sweazland ɗin sa, babu tsammani ya ganta a gabansa, ta riƙe rigarsa tana girgiza masa kai cikin tsananin tashin hankali. "Idan ka kashe shi, rufe mini kai za ayi, ba lallai na sake ganinka, ka yi haƙuri kar ka yi kisan kai dan Allah" Jikinsa tsuma kawai yake yi, ya aiwatar da abun da zuciyar sa take raya masa, saboda yadda haɗin da yayi amfani da shi, yake fizgar kansa yake jin sa tamkar jinjirin doki, zuciyarsa kuma kamar an kunna wuta. Ta rirriƙe hannun da ya riƙe wuƙar da shi, da hannu ɗaya ya yi jifa da matashin gefe, shi kuma ya saki wuƙar, sai tangaɗi yake yi, ya kasa tsayuwa, sai gumi da yake tsatsafo masa ya furta "Madaki" kawai ya yanke jiki ya faɗi, sai a lokacin ta ga uban saran da yake gadon bayansa, ashe duk abun nan an sare shi a baya, rigarsa ta rine da jini ta baya. Wani irin gigitaccen kuka ta saki, ta ce "Na shiga uku, dan Allah ku taimaka mini a kai shi asibiti" tayi maganar tana girgiza shi. Ya kalleta da idanunsa, suka yi jawur, jikinsa ya fara rawa ga gumi ya jiƙa masa fuska. Ragowar mutanen da suke wurin, suka dare suka bar ta da shi, a wurin. "Master dan Allah kar ka rufe idonka, yanzu zamu tafi asibiti, Allah ka kawo mini ɗauki, Allah ka duba lamarin nan". Guduma ne ya shigo cikin layin da gudu, ya jefar da makamin hannunsa ya ƙaraso, wata irin ajiyar zuciya ta saki, yana zuwa ya jijjiga Al'amin ya ce "Master" sai dai idanunsa sun lumshe, saboda jinin da ya zubar. Yayi ƙoƙarin ɗaga Al'amin, ya saɓa shi a kafaɗarsa, amma abu ya gagara, ba ƙiba ce da shi ba, sai dai akwai nauyi. Ya kalli Jauhar da ta rikice, take ta kuka ya ce "Anty ki kwantar da hankalinki, in sha Allah yanzu zamu kai shi asibiti". Ya din ga wani irin fito, kan ka ce kwabo, wasu matasa suka din ga ɓullowa da ɗaya ɗaya, su ma suna fiton wasu suna fitowa. Suna zuwa suka yi tara-tara suka sunkuci Al'amin, guduma ya saɓa shi da ƙyar, suka nufi titi. Da ƙarfin tsiya suka ƙwaci 'yar ƙurƙura a titi, suka ce mai ita ya bi su Asibiti ya karɓa. Sai dai da suka je, ma'aikatan lafiya, suka ce ba za su karɓe shi su duba shi ba, sai da jami'an tsaro. Cikin kuka ta ce "Dan girman Allah kar ku yi mini haka, ku ceto ransa kar ya rasa ransa, dan Allah ku fara duba shi, kan a kawo 'yan sandan" ma'aikatan suka ƙeƙashe ƙasa suka ce, sai fa jami'an tsaro sun zo". Ta din ga rusa kuka a cikin emergency, guduma sai bata haƙuri yake yi. Ta kasa jurewa, ta tashi ta bi wani likita, ta riƙe rigarsa tana kuka ya ce "Dan girman Allah ka ceto rayuwar mijina, kar a rasa ransa dan Allah" Ya ce "Ba laifina bane ba, dole mu san meyafaru kafin mu taɓa shi". Kan kace kwabo, sashen emergency ya cika da 'yan daba, saboda an kawo al'amin. Babu tsammani ta ga shigowar liti tare da Walid, da wasu tawagar marasa jin suna take musu baya. Suka ƙaraso, in da jauhar ke zaune, da Al'amin a gabanta. Walid ya ce "Madam, ya aka yi haka ta same shi?" Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, kawai ce mini aka yi ana faɗa, na je na tarar da shi, da zai cakawa wani wuƙa amma ya fasa, kawai dai ya ce madaki ya faɗi ashe an sare shi, kuma sun ƙi duba shi wai sai ƴan sanda sun zo, dan Allah ka saka baki yaya Walid. Ya kalli liti ya ce "Zan ɓallo ruwa, a toshe magudanan daga waje" liti ya jinjina kai, ya ja guduma suka fita. Wasu daga cikin matasan suka shigo, suka koro wasu daga cikin majinyata waje, suka ritsa likitoci da makamai, sai sun duba Al'amin. Aka ce su kai shi kan gado, Walid ne ya ɗauke shi, suka kai shi kan gado, saran da aka yi masa ba ƙarami bane, yayi zurfi, hakan ya ƙara razana Jauhar. Liti ya ce "Wannan yankan madaki ne yayi masa shi, wannan shegiyar wuƙar da aka ce ta tsafi ce, da ita yayi masa saran". Jauhar ta ce "Na shiga uku, ba zai tashi ba kenan?" Walid ya ce "Zai tashi ki kwantar da hankalinki" Aka yi wa Al'amin ɗinki, kamar ƙwarya aka ɗinke bayansa, sai dai walid ba su bari an yi a gaban jauhar ba, aka ɗibi jininsa, dan dubawa idan sai an ƙara masa jini, sai dai baya buƙatar ƙarin jini, sai dai an saka masa ruwa saboda jirin da yake yi ya hana shi tashi. Ana tsaka da duba shin, jami'an tsaro suka iso, Walid ya ce kar matasan nan su bar su su shigo, sai an gama yi masa komai. Aka din ga artabu da 'yan sanda da dandazon, yaran da suka yi wa harbar emergency ƙawanya, da kyar 'yan sandan suka shiga. Da ƙyar aka tarwtsa tarin matasan nan, tana zaune ta ƙurawa fuskarsa ido, ƴan sanda suka ɗauki statement ɗin abun da ya faru. Jauhar sai addu'a take yi, tana fatan Allah ya sa ya farfaɗo. Ta riƙe hannunsa, tana shafawa a hankali ta ce "Allah ya shirya mini kai, ya baka lafiya master, inuwarka ce kawai nake tsaye a ciki nake saka ran samun farin ciki, dan Allah ka daina zuwa ana cutar mini da kai" Idonsa a rufe, ya ɗaga hannunsa a hankali, ya shafi fuskarta sannan ya buɗe idon a hankali ya kalleta sai dai bai yi magana ba. "Sannu master, an yi maka ɗinki a bayanka, akwai abun da yake yi maka ciwo ne?" Ya girgiza kai almar a'a. Ta shafi sumar kansa ta ce "Allah ya baka lafiya" Juyi yayi a hankali, ya kwanta a kan cinyarta, muryarsa ƙasa-ƙasa ya ce "Idan kina kuka ciwon ƙara zafi yake yi" ta goge hawayenta ta ce "To na daina, amma idan aka ji maka ciwo, zuciyata ce take kuka ba na so master" tayi maganar hawaye na kwarara daga idanunta. A hankali yake matsa hannunta, yana jin wata nutsuwa ta mussaman, da sassaucin zafin da zuciyar sa take yi masa. Zuwa magariba, ya miƙe ya ce sai sun tafi gida, Jami'an tsaro suka ce za su tafi da shi, sakamakon tayar da tarzoma a unguwa. Walid ya ce "Saboda hauka ake yi, master ku ware gida, ni ku tafi da ni mu muka je muka tayar da tarzomar" Ana fito da Al'amin, guduma ma ya taso, da sauri, Al'amin daga shi sai dogon wando, suka tari napep suka tafi gida. A wurin maman halimatu jauhar ta karɓi mukulli, ta buɗe musu gidan suka shiga. Ta saka yayi wanka, yayi alwala ya rama sallolin da ake bin sa, ta kawo masa abinci ya ci. "Master" ya kalleta "Dan Allah ka fita daga shirgin madakin nan, ba shi da imani, kar ya hallaka ka dan Allah" Ya girgiza kai ya ce "Sai dai ɗaya yayi ajalin ɗaya ko ni ko shi, shari'ata da shi, Allah ne kawai zai rabata" Cikin rauni ta ce "Ina haɗaka da girman zatin Allah" "Shhhh, ki daina haɗa ni da Allah, kin san nauyin abun da aya aikata mini?" "Ban sani ba, amma ina da yaƙinin koma me zaka yi masa, ba zaka huce ba, ka yi haƙuri ka bar wa Allah mana, idan wani abun ya same ka ya zan yi ne? Yanzu kalli halin da ka sakamu a ciki, na san yanzu haka a cikin pain ka ke, ciwon a jikinka yake, amma a zuciyata nake jin raɗaɗin, haba master, haba dan Allah" tayi maganar wasu zafafan hawaye na gangarowa daga cikin idanunta. Ya miƙa hannunsa ɗaya da ba a side ɗin ciwon yake ba, ya janyota jikinsa, ba ta musa ba ko yi masa gardama, ta kwanta sosai ta cigaba da kukan, tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa sosai, kasancewar babu riga a jikin sa. "Ba zan ɓoye miki ba, ban taɓa tunanin zan yi wata alaƙa da wata 'ya mace ba, saboda ina yi musu kallon azzalumai, ke ki ka fara canza tunanina". Al'amin Ibrahim shi ne cikakken sunan Al'amin, mahaifinsa haifaffen garin kano ne, gidansu gidan yawa ne, baban Al'amin shikaɗai ne a wurin mahafiyarsa da ta daɗe da rasuwa, sai tarin 'yan uba da galibinsu mata ne. Yayi karatu daga primary zuwa sakandare har yayi diploma, sai dai aikin yi ya gagara samuwa, akwai abokinsa sammani da suka yi karatu tare, tare suke yawon neman aiki, ya ja shi garin su tofa, aka samo musu gona, suka fara noma. A can ya haɗu da Zahra'u, ya ce yayi mata, da fari tsokanarta yake yi, saboda kwalliyar da take yi ta 'yan ƙauye ce take bashi dariya, daga baya soyayya ta ƙullu a tsakaninsu. Abu kamar wasa, har ta kai ga aure, duk da bashi da wata ƙwaƙƙwarar sana'a, sai kame-kame. Sun sha gwagwarmayar rayuwa tare, sun yi faɗi tashi, sun yi fama da yanayin rayuwa, kafin Allah ya buɗa masa ya fara samu. Lokacin da suke cikin wahala babu mai taimakonsa, daga shi sai ita suke wahalar su, ta samu ciki a lokacin ta haifi ɗan ta na fari, aka saka masa Abubakar Assidiƙ, sai lokacin da Allah ya fara buɗa masa, 'yan uwansa suka saka musu ido, da surutun yana zaƙewa da yawa a kanta. Komai ya samu ita, ya tashi daga tsakiyar cikin garin kano, ya koma gwauron dutse yayi mata gida mai kyau. 'yan uwansa suka fara tsangwamar ta, da cewa ta shanye musu ɗan uwa, Ibrahim ya mayar da ita makaranta ya samo mata admission a FCE, ta ke karantar English islamic. Kasancewar ta mace mai kyauta, da fara'a da sakin fuska ga mutane, ya sanya take da masoya sosai. Sai dai duk da kyautarta, da son mutane dangin mijinta ba sa ƙaunarta. A can gwauron dutsen, ta haɗu da wata mata rahila, maƙwabciyarta ce, tana yawan zuwa ta kawo mata complain a kan mijinta ba ya kula da ita da yaranta, hakan ya sanya tausayin rahila ɗarsuwa a zuciyar Zahra'au, kusan kullum cikin yi wa rahila aike take, na abun da zata kula da yaranta, kuɗi, sutura, abinci kayan masarufi, saboda Ibrahim yana sakar mata sosai baya yi mata iyaka da komai. Tana NCE 2, Sadik ya shekara biyar, ta samu ciki, tayi ta fama ga laulayi ga karatu, rahila take barwa Abubakar ta tafi makaranta, ƙarshen wata, take biyanta da kuɗi mai kauri saboda ita ma ta samu. Ta haifi ɗanta na biyu, aka saka masa Muhammad Al'amin, saboda haihuwar maza da take yi, dangin miji, suka ƙara yi mata caaa wai tana ta haifar maza, dan ta kwashe komai na gado idan ya mutu. Tana iya ƙoƙarin ta wurin saka Ibrahim ya yi kyautata musu su ma, amma ba sa gani sam. An yi shagalin suna sosai da aka haifi Al'amin, saboda yana tashen kuɗi a lokacin. Tana kyautatawa 'yan uwanta na ƙauye ma, ciki har da sauran danginta da 'yan uwanta. Rahila ta shiga ta fita, ta zama ƙawar Zahra sosai da sosai, Ibrahim ba ya ɓoye son da yake yi wa zahra, dan ko a gaban waye ko sun yi faɗa ba ya canza mata suna daga baby Zahra, ciki har da gaban 'yan uwansa. Makaranta mai tsada sosai ya saka Abubakar, tun Al'amin bai cika shekaru uku ba, shi ma aka saka shi, saboda kukan da yake yi idan Sadik ya tafi makaranta. Akwai soyayya mai ƙarfin gaske da shaƙuwa, a tsakanin Abubakar da Al'amin, cikin soyayya da kulawa suke rayuwarsu a tskanin Abbu da ummin su. Ibrahim ya biya wa kansa umara, ya je da shi da Sadik, shekara ta zagayo, ya biya wa Zahra da Al'amin suka tafi, hakan ya ƙara hiafar da cecekuce a tsakanin dangin Ibrahim, wai saboda tsabar mugunta, ya biyawa yaran da zuwansu umara makaruhi ne, alhalin su ga su. Sai dai a lokacin da suke maganganun, a lokacin yake ƙara nuna wa duniya irin son da yake yi wa Zahra da yaransa, a cewarsa ita ta juri tsantsar talaucinsa, yanzu kuwa dole ta huta fiye da kowa. Ta kammala karatun ta, ya ce sai ta juya degree, ta ce ta gaji, hutawa za ta yi, ya ce bai yadda ba. A lokacin ba ta da wata aminiya da ta wuce rahila, rahila ta yi ta cewa kashe aurenta za ta yi, saboda ta gaji da zama da mijinta baban su Abba, Zahra tayi ta rarrashinta da nuna mata illar hakan, ta ƙara ƙaimi wurin taimakawa rahila, dan kuɗin makarantar su ma, ita take biya, tana bawa Rahila haƙuri a kan ta zauna ta kula da yaranta. Dangin Ibrahim tsanar da suke yi wa zahra'u, suka haɗa har 'ya'yanta, suka din ga cewa asiri ta yi masa ta mallake shi. Duk ƙoƙarin da Zahra ke yi a kan rahila, sai da ta kashe auren nan, ta ce ba zata iya ba ta gaji da rayuwar matsi, zahra ta sha bata labarin wahalar da suka sha, kan Ibrahim yayi arziki sun sha kwana fiye da uku, ba su ɗora tukunya ba, amma ta ƙi fahimta. Ibrahim yana ta fafutukar, ta tafi bautar ƙasa, ta hau laulayin wani cikin, dan ma Allah ya taimake ta, ba ta ɗaukar ciki a kai a kai, dan lokacin, Al'amin ma ya kusa shiga Jss1 Abubakar yana da shekaru goma sha biyar. Ta haɗu da ciki mai laulayi sosai da sosai, hajiya mamanta ta ce, ta koma gida ko wata ɗaya tayi, a kula da ita, Ibrahim ya ce tayi haƙuri, a bar masa matarsa yana kula da ita. Rahila tayi ta zuwa tana yi mata aikace-aikace, da kula mata da su Abubakar. Sadik da Al'amin su na da banbancin halaye, Sadik yana da haƙuri, da fara'a kamar ummin su, Al'amin kuwa sa ne, ba ka dariya sai hamma. Ba ya fara'a ko wasa a cikin yara baya yi. Idan kuwa yayi wasa cikin yara to tabbas sai wani yayi kuka, domin kuwa wasansa na kasada ne, kwaikwayon tsalle-tslle, da wrestling shi kawai yake yi. Idan ka ga yana wasa wasu lokutan, ko yana dariya, tare da Abbu ne, ko Abubakar, Ummin ma faɗa suke yi, saboda tana yi masa faɗa a kan, rashin jin da yake yi na kasada. Tun da suka ga Ummi da ciki suke murna, Abbu ya ce musu, baby girl za a haifar musu, Al'amin ya din ga murna, shi ma za ayi masa ƙanwa, yana son ya ga yana da ƙanwa mace, ya din ga hasaso irin kulawa da gatan da zai yi mata. Yana jss1 sport master ɗin su, ɗan karate ne, Al'amin ya takurawa Abbu yayi masa register a makarantar karate, Ummi ta ce ba ta so, ya daina biye wa Al'amin, amma ya ce mata ba a dankwafe yaro. Ta sha wahalar cikin nan sosai, da ya isa haihuwa, sai tiyata aka yi mata, aka ciro baby girl mai kama da ita, tun a asibiti ya ce sunan zahra zai saka mata. Nan ma 'yan uwansa suka hau surutun, bai saka sunan uwarsa da ta mutu ba, sai na mace, macen ma 'yar ƙauye. Al'amin ya ƙallafa ransa a kan jaririyar nan, ko Sadik da yake yayansa, sai ya yi da gaske yake bari ya ɗauketa, 'yan barka ma rashin mutunci yake yi musu, ya ɗauketa ya ƙanƙame ya haɗa rai yana muzurai, ba za a ɗauketa ba. Ana ta shirin suna, jikinta yaƙi daɗi daga ita har jaririyar, jaririyarma jaundice ya kamata, sai da aka sakata a kwalba, kwananta biyu 'yar ta koma ga Allah. Al'amin ya shiga tashin hankali, ko abinci ya ƙi ci, saboda yadda Allah ya saka masa son yarinyar. Zahra ta din ga wani irin zazzaɓi, haɗe da jijjiga, sai da aka kaita ɗakin duhu, an kaita da daddare da asuba ita ma ta koma ga mahaliccinta. Tamkar ƙaramin yaro, haka Ibrahim ya din ga kuka, ya fita hayyacinsa, duk da ƙanƙantar shekarun Al'amin, ya san mutuwa, ya san idan aka yi ta ba a dawowa. Sai dai ya kasa kuka, baya magana, baya cin abinci, saɓanin sadik da ya din ga kuka, da yawa sun ɗauka tsabar taurin rai ne, na Al'amin ya sanya ya ƙi yin kuka, sai dai a kwana na uku da rasuwar zahra'u, aka wayi gari aka tarar ya sassanƙare, jikinsa babu numfashi. Shima aka kwashe shi zuwa asibiti. Ibrahim da sadik, suka ƙara shiga matsanancin tashin hankali da kiɗima, sai Alhaji sammani da dangin zahara'u da rahila, su ke ta damuwa. Sai da Al'amin yayi sati biyu a asibiti, ƙarƙashin kulawa ta musamman, bai taɓa zaton haka yake ƙaunar ummi ba, haka yake sonta ba sai bayan ta mutu. Aka watse daga zaman makoki, Hajiya ta ce "A bata su Sadik ta tafi da su, kan ya samu yayi wani auren". Nan ma ya ce shi dai tayi haƙuri ta bar masa yaransa. Ta ji haushin hakan, saboda a ganinta ita ma 'yarta ta rasa, yakamata ko yaya a ɗan bata yaran za ta ji daɗi. Ya zamana daga shi sai su a gidan, wtaran haka yake saka su a gaba, yayi ta kuka, Sadik yana taya shi, Al'amin kuwa sai dai ya kom gefe yayi shiru idanunsa sun yi jawur, yayi ta ciwon kai. Ibrahim ayi musu wanka, ya kai su makaranta, lokacin tashi, ya baro kasuwa ya zo ya kai su restaurant su ci abinci, su shirya zuwa islamiyya. Sanin halin 'yan uwnasa ya sanya ya fito da duk wani abu, da abu da ya san mallakawa zahara'u, ya ce a raba wa su Al'amin, shi ya yafe gadon. Nan ma ya sha caccaka da baƙaƙen maganganu, gaba ɗaya walwalar gidan ya zamana babu, rahila ta tsiri sintiri, da zuwa ganin su Sadik, ta yi musu hidima, Ibrahim ya nuna mata ba ya so, ita kuma ta ce saboda Allah take yi, da zumuncin da yake tsakanin su da Zahara. Sai dai a gefe, ta fara shiga malamai, dan ya auret, ta bi ta wurin sammani abokinsa, a kan ya lallaɓa shi ya aureta, ta kula da yaran Zahra'u, ita dai tana ƙaunar su fisabilillahi. Sammani kuwa ya wuce mata gaba, duk da Abbu ya nuna ba ya so, shi hana cikin alhinin rashin matarsa, amma tasirin sihiri, da yadda sammani ya din ga lallaɓa shi, da nuna masa saboda yaran zai yi auren, ya haƙura ya auri Rahila, ta tare da nata yaran har su uku. Hajiya ta ji haushin hakan, ta san alaƙar rahila da Zahra'u, amma ta so ko yaro ɗaya ya bata, saboda Zahra ce kawai ta rage mata, sai da ta binne 'ya'ya bakwai, ita ma da ta tsaya, ta koma ga Allah sai ƙanwarta guda ɗaya da suke uba ɗaya, baban su ya rasu babarta ma da ta kasance abokiyar zamanta ta mutu ta bari, ta riƙeta kamar 'ya. Da fari kamar gaske, Rahila take kula da su, dan sadik ya fara sakewa da ita, tun da dama sun santa, ban da Al'amin da mutuwar umminnsu ya ƙara masa miskilanci. Aka shafe shekaru uku, ko ɓatan wata ba ta yi ba, duk da tana kamantawa, amma ba ta iya ɓoye banbancin su da 'ya'yan da ta haifa. Ibrahim ya riƙe mata nata yaran, ganin nasan ma suna samun kulawa daga gare ta Sannu a hankali, ƙawaye da dangin Ibrahim, suka nusar da ita, duk wannan wahalar da take yi, a banza, tun da ba ta haihu da shi ba, kuma yaransa maza ne, dan haka ta nema wa kanta mafita. Nan ta ƙara riƙe wa bin bokaye wuta, ta fara ƙoƙarin cire wa Ibrahim son yaransa, saboda yadda yake tsara irin rayuwar da yake son ɗora su a kai, duk da yana kamanta yi mata kara a kan 'ya'yanta kamar nasa, amma yana nuna wa su Al'amin so, mussaman Al'amin da yake ƙarami, kusan kullum yana tare da shi, wataran ya ƙi cin abinci, sai ya zaunar da shi ya bashi, ko ya kwana da shi wuri ɗaya, saboda ya ɗebe masa kewa. Wannan soyayar ba ƙaramin ƙular da rahila take yi ba, dan haka ta zage, da shiga da fita, a hankali soyyayar da yake yi musu, ta fara ja baya, ta fara wulaƙanta su, tana hantarar su, ba ta tsaya a nan ba, ta haɗa da hana su abinci. Sadik take iya sarrafawa, yadda take so, ban da Al'amin, da kome za ta yi masa ba zai yi abun da take so ba. Ibrahim ya zo ba ya iya cewa komai, azaba iri-iri, duk wani laifi da Al'amin zai yi, Sadik zai karɓi hukuncin, ba ya ƙaunar ya ga an taɓa masa Al'amin. A haka ta samu ciki, tana murna tana fatan ta haifi namiji, ta haifo 'ya mace,  wato shahida. Ba haka ta so ba, amma ko ba komai dai hankalinta ya kwanta ta haihu da shi. Ta frara yi wa su Al'amin horon yunwa, tunanin Sadik, yaya zai samo abun da zai bawa Al'amin, ƙiri-ƙiri da gatansu, amma Sadik har jari bola yake yi, saboda ƙaninsa, ya san Al'amin ba ya ga maciji da yunwa ko kaɗan. Mutanen unguwa suka fara surutu, amma tayi burus da su, a lokacin ne suka sake komawa cikin gari ɗan agundi, saboda matsalar da Abbu ya samu a kasuwa, na damfara da aka yi masa amma gida suka koma mai kyau shi ma. Ta saka Abbu ya ɗaukar mata yaranta, Abba da Nazir yake tafiya da su kasuwa, amma ta hana ya din ga tafiya da su Sadik, lokacin Sadik yana da shekaru ashirin, Al'amin kuma sha biyar. Ta saka ya cire su daga makarantar kuɗi zuwa ta gwamnati, ta nu na wa 'yan uwansa ta fi su iya barikanci, ɗan tallafi duk da yake ba su ta hana gaba ɗaya. Hajiya sai dai ta zo ganin su Sadik, ba za a taɓa barin su, su je in da take ba, wani zuwa da tayi ta shiga tashin hankali, ganin Al'amin na yawo ko takalmin sawa babu. Ta ce "Rahila ki ji tsoron Allah, zumunci bai ce haka ba, wane irin riƙo ki ke yi wa yaran nan haka?" Ta kada baki ta ce "Irin riƙon da ya dace da su mana, idan bai yi miki ba ki kwashi tsiyarki ku koma ƙauye" Ibrahim ya dawo, ta kitsa masa ƙarya da gaskiya, ya ce wa Hajiya kar ta sake zuwa, idan yakamata ya sako su a gaba ya kawo mata su ta gansu. Tana kuka Sadik na kuka, ta koma, ta ce da yardar Allah, ba zata sake taka gidan ba, da sunan zuwa ganin su Al'amin. Al'amin duk ranar da yake jin yunwa, sai ya kwanta ya ce ba shi da lafiya, ba za shi makaranta ba, aikin ƙarfi babu wanda Sadik baya yi, saboda kar Al'amin ya zauna da yunwa saboda ya san baya jureta ko kaɗan. Ta kai ta kawo, Rahila har sakawa take Abbu ya kama Sadik ya zane shi, dama Al'amin ba ya taɓuwa, tun ranar da ta saka aka dake shi, Abbu na fita, ya kama Nazir a waje, yayi masa dukan kawo wuƙa, duk wani skills da yake samu, a wurin karate ya sauke su a kan Nazir da ya ma ɗan girme shi. Amira kuwa bala'in tsoronsa take ji, tun da ya taɓa ball da ita, ta targaɗe hannu. Rayuwa ta cigaba a haka, har Al'amin ya yi candy, Sadik ya tsaya tsayin daka, ya shiga polytechnic. Abbu ya bar su babu sana'a, ba abun yi, ya cire hannunsa daga kan karatunsu, amma ya ɗauki agololi ya kai kasuwa. Ana haka 'yan daba ƙanana masu tasowa suka addabawa unguwar , su yi sare-sare, ko su je su tsokano 'yan wata unguwar. Ga Al'amin da yawon tsiya, idan yayi dare sai Sadik ya fita nemansa, idan ya gano shi da ƙyar suka dawo gida, sai su tarar Abbu ya rufe gida, wai sun tafi yawo, su koma in da suka tafi su kwana. Rayuwa ta yi wa su Al'amin tsanani, ga rashin uwa, ga ƙiyayyar uba, da makircin matar uba, ga ƙiyayyar dangin mahaifi, dangin uwa kuma sun watsar da su. Aka zaɓi Al'amin a cikin matasan da zasu je youth game, su wakilci Nigeria, Rahila ta ziga Abbu ya ce ba za shi ba. Aikuwa ya zuciya, ya bar gidan, ya ce barin garin zai yi, Sadik ya dawo yana nemansa, Amira ta gaya masa abun da ya faru, ya bazama neman Al'amin, da ƙyar ya gano shi, ya lallaɓo shi suka dawo gida, Amma suka tarar Abbu ya rufe gida, ya ce shi ma Sadik ɗin ya bi Al'amin su bar duniyar ma gaba ɗaya ba garin ba, ba ɗan iska bane shi, da za su din ga dawo masa gida bayan goma na dare. Sadik ya din ga rarrashin Al'amin, da ya riga ya zuciya, ya samo musu aron tabarma, suka shimfiɗa suka kwanta a waje, Cikin dare aka tashi faɗan daba, suna cikin bacci Al'amin ya ji an buga masa abu a ka, ya tashi a gigice, bai gama wartsakewa ba, aka danƙo shi, za'a soka masa almakashi, Sadik ya tashi a rikice, ya riƙe almakashin ya ce "Bawan Allah me muka yi muku? Mu ba 'yan daba bane" "Amma ai 'yan unguwar nan ne ko? Fansa muka shigo ɗauka, dan haka duk kan wanda azal ta faɗa shikenan" ya fizge Almakashin ya soka wa Sadik a cikin sa! Maimakon Al'amin. Ayshercool 08081012143 36 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Ya saki Sadik a ƙasa bayan ya caka masa almakashin, cikin tsananin tashin hankali, Al'amin ya yi kukan kura ya danƙi ɗan daban, amma wani daga cikin yaransa, ya lallaɓa ya sake maka masa gora a baya, ya gantsare yana wani irin ihu, suka yi gaba suka bar su. Ya din ga dukan gate ɗin gidan, yana ƙwalawa Abbu kira, ya koma kan Sadik, ya rungumo shi, yana jijjiga shi. Sai da garin yayi shiru, sai kururuwar Al'amin yana kiran Yaya. Maƙwabcinsu ya fito, na kusa da shi ma ya fito, aka din ga buga gidan su Al'amin, har aka tafi nemo mota, sannan Abbu ya buɗe. Sai dai ya shiga tashin hankali, ganin Sadik a kwance kamar mara rai. Cikin tashin hankali Abbu ya tafi kici-kicin fito da mota, Al'amin ya zuciya ya ɗauki Sadik a kafaɗarsa, kawai yayi gaba. Da ƙyar aka riƙe shi, aka saka Sadik a mota. Al'amin sai zubar da hawaye yake yi, ya na kiran "Yaya ka buɗe idonka ka kalleni, ka tsaya yanzu zamu je asibiti" "A galabaice, Sadik ya motsa ya riƙa hannun Al'amin, sai kuma hannunsa ya saki. ko da suka je Asibiti, aka tabattar musu da Sadik ya koma ga Allah. Al'amin ya durƙusa a kan gawar, ya din ga rusa kuka, kukan da ko lokacin da umminsu ta mutu bai yi shi ba, maƙwabta na ta rarrashin Al'amin. Cikin kuka Abbu ya ce "Al'amin komai ya samu ɗa na kai ne sila, ka sa nayi rashin ɗa mai biyayya" "A'a Alhaji Ibrahim, kar ka sake ka ɗorawa Al'amin laifi, kai ne babban mai laifi, kana sane sarai unguwar nan babu kwanciyar hankali, ka bar su a waje, da ka buɗe musu sun shiga gida, koman dare ai da haka ba ta faru ba". A daren aka yi wa Sadik sutura, Al'amin gani yake yi kamar a mafarki, awannin da suka gabata suna tare amma a yanzu wai babu Sadik. Kodayeke Abbu yana da gaskiya shi ne sila, da bai ce zai bar gidan yayi tafiyarsa ba, da haka baya faru ba, dan kuwa Sadik ba ya yawon dare. Har jami'an tsaro sai da suka zo suka ɗauki bayanan abun da suka faru, sai dai Al'amin ya kasa magana. Sadik ya tara ɗimbin mutane, yara da manya matasa da dattawa wurin sallatar gawarsa, kasancewar sa mutumin kirki. Al'amin ya ji ina ma shi aka kashe, Sadik ya rayu, yayan nasa guda ɗaya tal da yake saukewa duk wata damuwarsa ya ɗauka babu ƙosawa ko gazawa, an kashe masa shi. Alhaji sammani, ya yi wa Ibrahim tatas, a kan yadda ya koma soko a kan gidansa, tare da ci wa Rahila mutunci tsaf, a kan abubuwan da take aikatawa. Ƙarshe ta shiga ta fita, ta raba abotar da aka yi shekaru ana ginata, suka rabu dutse a hannun riga, suka yi uwar watsi. Depression ya nemi ya kama Al'amin, babu wand yake ta tasa, gashi yanayin halayarsa idan ba wanda ya sanshi ya saba zama da shi ba, ba kowa zai iya masa ba, saboda miskili ne, ga nuƙufurci, ba zai taɓa cewa wani ga damuwarsa ba, shi ba abokai ba, haka ya din ga ragaita a layi, raɗaɗin mutuwar Sadik taƙi barinsa. Ya tafi wurin 'yan sanda ya tambayi, ko sun kama wanda ya kashe yayansa, suka ce masa bincike suke yi a kai, dan har a lokacin ba su tabattar da wanda yayi kisan kan ba, kuma a ranar ba Sadik kawai aka kashe ba. Al'amin ya koma gida, yayi ta addu'a Allah ya sa a kama wanda ya kashe masa Sadik, duk da dare ne, amma a ko ina ya ga wanda ya kashe shi zai gane, dan kuwa ƙofar gidan su akwai security light. Duk bayan kwana biyu sai Al'amin yaje, tun suna sauararsa har suka fara korarsa. Ga matsi ya ƙaru daga gidansu, babu in da zai samu abinci, ya yanke shawarar fara zuwa kasuwa ya duba ko dako ya fara, sai da ya je ya tarar ashe dakon ma sai ka san wani, sai an san da kai, duk sana'ar da yayi tunanin farawa sai ya ga dole sai da jari, gashi Rahila ta cigaba da ziga Abbu, ya ƙara tsanar Al'amin wai shi ne silar mutuwar Sadik. Al'amin ya fara gajiya da yunwa da take neman tagayyara shi, ya fara zuwa gida ya ɗauki duk abincin wanda ya tarar ya cinye, idan ya tafka wannan tsiyar, sai ya gudu ya kwana a kangwaye, gashi ya koma HND tun Sadik na raye, dama shi ne yake ta fafutukar tara school fees ɗin sa kan ya rasu, yanzu kuma ga yunwa da rashin kuɗin transfort dan haka ya daina zuwa makaranta gaba ɗaya. Gashi ko a maƙwabta aka rasa wanda zai yi wa Abbu nasiha, ko su din ga taimakonsa, saboda ana ganin babansa yana da rufin asiri. Yana can garin yawonsa, kawai ya hango wanda ya kashe Sadik, a tsallaken titi, da tawagar matasa 'yan daba, da gudun gaske Al'amin ya tsallaka titin, sai dai kan ya ƙarasa sun ɓace masa, cikin tashin hankali ya ƙarasa wurin wani mai ice ya ce "Malam dan Allah wanda ya wuce ɗin nan ina yayi?" Ya kalli Al'amin ya ce "Meye haɗinka da shi?" "Yayana ya kashe da almakashi, bai yi masa komai ba, 'yan sands suna ta nemansa" "Taɓ, ka raba kanka da wannan. Madaki kenan gawurtaccen ɗan daba ne, hukuncin kisa ma aka yanke masa a gidan yari, amma muka ga an sake shi, duk ya gallabe mu, ya hanamu sukuni mu ma, sai dai ka bar wa Allah kawai" Ai Al'amin bai tsya jin ƙarshen zancen ba, ya shiga cikin unguwar ya din ga yawo, amma bai ga madaki ba. Washegari da sassafe, ya koma wurin 'yan sanda ya gaya musu ya ga wanda ya kashe yayansa, su tafi tare da shi a nemo shi, an gaya masa sunansa madaki. Wani ɗan sanda ya kada baki ya ce "Ka san mutum nawa madaki ya kashe aka ƙyale shi?" al'amin ya ce "Ni ina ruwana da mutum nawa ya kashe, ku kama shi a kai shi kotu ni dai". "Ko an kai shi ma, za a sake shi, ka je ka yi haƙuri haryanzu bamu tabattar da shi ya kashe shi ba". Kasancewar Al'amin yana kan tashen balaga, ya sanya ya tsaya yana yi musu rashin kunya, aka saka wani sageant, ya zane shi aka kore shi. Hakan yayi matuƙar tunzura zuciyar Al'amin, ya din ga jin jinin ɗan uwansa ba zai tafi a banza ba. Ya din ga sintiri a unguwar da madaki yake, kasancewar ba su da nisa sosai, ya samu duk bayanin da yake son samu a kan madaki, da in da yake zama da shi da yaransa. Ya je gida ya shiga kitchen ya samo, wuƙa sabuwa gal, ya je ya ɓoye, ya saka a ransa shi ma sai ya kashe madaki, ko da kuwa za a kama shi a kashe. Sai dai aka yi rashin sa'a, Madaki bai fiye zama a unguwar ba, sai idan zai shigo yayi rashin mutunci, Al'amin ya din ga fakonsa, har ya yi wataran sa'a ya tarar yana nan. Gadan-gadan ya ratsa tarin matasan da suke ɗauke da makamai suna shaye-shaye, ya nufi madaki da wuƙa. Matasan suka mimmiƙe, amma madaki ya ɗaga musu hannu, a kallo ɗaya madaki ya gane Al'amin. Kafin ya ƙarasa gaban madaki, sani ya sanya ƙafa ya taɗiye Al'amin dan haka ya faɗi a gaban madaki, suka kwashe da wata irin dariya. Al'amin ya yinƙura zai tashi, madaki ya saka aka take masa kafaɗun Al'amin da ƙafa, yana ƙoƙarin tashi, amma cikin ƙarfin Al'amin ya tashi, madaki ya tako gaban Al'amin ya shaƙe wuyansa. Take Al'amin ya ji kamar an shaƙe shi da wata muguwar sarƙa mai nauyin gaske, a take ya ji numfashin sa na neman ƙwace masa. Al'amin ya saki wuƙar ya koma kokowar raba hannun madaki da wuyansa, madaki ya tsare shi da jajayen idanunsa da ya rambaɗa musu farin kwallin tsafi, yana ƙyaƙyata wata uwar dariya, daga bisani kuma ya tsuke rai tamau, ya ƙara tsananta shaƙe Al'amin, sai da ya ga ya daina motsi, sannan ya watsar da shi a wurin, ya kalli wani ya ce "Ku kai shi arear su ku watsar" "Ba za a saita ma hanya daga duniyar ba ya ci bulus kenan?" Madaki ya girgiza kai ya ce "Yana cikin tsananin ɗacin rashin ɗan uwansa, idan aka yage shi daga sararin nan, hutawa zai yi, sai ya gane kuskuren da ya aikata na yinƙurin da yayi" Suka ɗauki Al'amin suka kai shi unguwar su, suka jefar da shi a sume a gaban wani mai kayan miya, suka ce wa mutanen wurin "Gashi nan, ajiyarmu ne, zamu din ga bibiyar sa ku kira tsohonsa ya ɗauke shi idan yan buƙatarsa". 'yan unguwa suka ɗauke shu, suka kai shi gida, Abbu yana nan, aka kwantar da shi a tsakar gida, ana shafa masa ruwa, mai kayan miya ya gaya wa Abbu abun da yaran madaki suka ce, aka shawarce shi a kan ya kai maganar wurin jami'an tsaro, amma Abbu ya ce babu ruwansa, tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka, shi bai aike shi wurin 'yan daba ba. Tun daga nan madaki ya mayar da Al'amin kamar karen farautarsa, ya saka rayuwarsa a gaba, wataran har cikin unguwar su yake aikawa, a nemo masa Al'amin, a kai masa shi har dabarsa, su casa shi da zalunci kala-kala, wai sa ya saduda ya nemi afuwar abun da ya yi wa madaki, dan ba a taɓa samun wanda ya yi abun da Al'amin yayi ba, ya rasto har dabarsa ya nemi ya kashe shi, yana ƙanin ƙanin bayansa. Al'amin ya kalli madaki ya ce "Ka yi kaɗan na nemi afuwarka, baƙin kare kuma in sha Allah sai na zubar maka da jini, kamar yadda ka zubar da jinin ɗan uwana da bai yi maka komai ba" Ya durƙusa ya soka wa Al'amin wata kibiya a cinyarsa, cinyar sa na zubar da jini, amma saboda azabar taurin kai, ya datse haƙoransa ya ƙi ihu. "Na fuskanci zaka yi mini amfani, na saka ka cikin yarana daga yau, zaka din ga yi mini aiki" Al'amin ya girgiza kai ya ce "Ni fa kallon kare nake yi maka, da na bika gara na yi mutuwar wulaƙanci" Ya ce "Shikenan zamu gani, dafin ciwon da nayi maka na fili da na zuciya ya isheka ka saduda". Al'amin ƙafa taƙi takuwa, sai da kyar, ya din ga tagayyara a gari, yaran madaki suka matsawa unguwar su Al'amin, duk da suma suna da ƙasurguman 'yan daba, amma ba sa shiga harkar faɗan matasan 'yan daba. Al'amin ya ƙi ya karaya ya saduda, ga ƙafa yana ɗingisawa, ga yawon neman in da zai ci abinci, kullum rahiila cikin gaya wa Abbu take, Al'amin abubuwan da yake da yadda 'yan daba suke kawo masa farmaki, sun tabbatar da cewar shaye-shaye ya fara yi, dan haka lallai ya kori Al'amin daga gidan, ya daina zuwa kan ya kuma janyo musu wata masifar, ta ce a kama masa shago a cikin unguwa ya bar kwana a cikin gidan, duk da dama ba kullum yake kwana a gidan ba. Wata ranar juma'a da yamma, Al'amin yana tafe yana ɗingisa ƙafarsa, yaran madaki suka shigo, da wasu irin mahaukatan karnuka, kuma kai tsaye suka sakarwa Al'amin su, gashi ba zai iya gudu ba, saboda ƙafarsa, suka dirar masa da cizo, ya din ga danƙar karnukan nan yana jifa da su, manyan karnuka ne sun kai biyar, wannan ya yage shi ta nan, wancan ya kai masa cizo ta nan, sai da suka ga yana neman fara halaka karnukan, ko su yi mutuwar kasko da su, sannan suka nufi Al'amin suka fito da makamai. Dan madaki cewa yayi, su kai masa wani sashe na jikin Al'amin sun cire masa. Karnuka sun yi masa kaca-kaca da kayansa, da fatarsa da cizo da yakushi, jikinsa duk jini, amma ya yinƙura ya tashi, ganin sun tsaya a kansa da makamai. Ɗaya ya shammace shi, ya sara masa wuƙa a cinya ta baya, ya hankaɗa shi ya faɗi, yana faɗuwa suka ga ɗaya daga cikinsu ma ya faɗi ƙasa jini na zuba daga jikinsa. Gaba ɗaya suka ɗaga kai suna kallon wanda ya yi aikin. Wani gabjejen mutum ne, baƙi mai jiki sosai, da jajayen ido, a yaran madaki wani ya yinƙuro, amma ya caka masa wuƙa a ciki shi ma, ya faɗi. Ya durƙusa ya ɗago Al'amin, jikinasa jina-jina, ya kalli wanda suke tare ya ce "Samo abun hawa, a kai yaron nan asibiti" ya kalli sauran yaran madaki ya ce "Ku je ku gaya wa madaki, ya zo dabata ni dodo babban sarki, ina nemansa. Na ji labarin irin ɓarnar da yake shigowa unguwar nan yana yi, kasancewar bana shiga shirgin shirmen ƙananan matasa, ya sanya ban damu ba. Sai dai na wuce a mota, a wancan lokacin na ganku kuna dukan yaron nan, wannan karon ma na ganku kun saka karnuka na cizon sa, kamar ba ɗan adam ba awanni ashirin da huɗu na bashi, ya zo yayi mini bayani, idan ya bari na taka na je in da yake sai dai uwarsa ta haifi wani. Ku ɗauke mini wannan mushen, ku ɓace daga gabana" jiki na tsuma, suka ɗauki wanda aka cakawa wuƙar suka tafi da shi. A asibiti ɗan wando kawai aka bar Al'amin da shi, jikinsa sai tsatstsafar da jini yake yi, saboda cizon karnuka da yakushi, ga raunin da yake ƙafarsa, sai da aka yi dressing raunukan jikinsa, sannan aka yi masa rigakafin cizon mahaukacin kare, dan ba a san wane irin karnuka ne suka ciji Al'amin ba, aka saka masa ruwa, sannan aka kawo masa lafiyayyen abinci daga restaurant. Dodo babban sarki, bai sake bi ta kan Al'amin ba, sai bayan magariba, ya je Asibiti da shi da yaransa, aƙalla dodo ya kai shekaru arba'in da biyar, ya girmi madaki sosai, madaki kuma ya girmi Al'amin. Ya tarar da Al'amin a zaune, hannunsa ana saka masa ruwa, ya ƙarasa gaban gadon Al'amin ya ce "Sannu ka ji" Al'amin ya jinjina masa kai. "Yaron nan ba shi da imani ko kaɗan, tayaya zai saka a sakarwa yaro karnuka su je shi, zai ci ubansa da ni yake zancen, zan gani zuwa dare idan bai zo ba, sai na kashe shi wallahi" ya sake kallon Al'amin ya ce "Kai ba kai ne kuka tare a unguwar nan shekarun baya ba? Kuna zuwa islamiyyar dogon bene, kai da ɗan uwanka ba?" "Ni ne" "Ina ɗan uwan naka? Meya haɗaka da madaki kuma, na ga kai ba irin su bane" Al'amin ya yi shiru, sannan ya ce "Kashe mini Sadik yayi, ba abun da yayi masa, ni kuma na ga ba zan haƙura ba sai na kashe shi nima" Dodo ya ce "A'a dama yayanka ne aka ce mini an kashe a layin dawaki? Madaki yana fama da gigin daba, tun da ya samu masu tsaya masa, ya je prison ya haɗu da wanda suka fi shi rashin mutunci yake abun da ya ga dama. Zan ci ubansa kuwa yanzu me ka ke son ayi masa gaya mini" Al'amin ya ce "Kawai sonake shi ma ya mutu, in soka masa almakashi kamar yadda ya yi wa Yaya" yayi maganar cikin damuwa. Dodo ya dafa kafaɗarsa ya ce "Kwantar da hankalinka, yanzu dai fatanmu ka samu lafiya, za aje a sanar da babanka, ya zo asibiti ya duba ka, a samu mai jinyarka" Ya girgiza kai ya ce 'A'a kar a gaya masa, zan koma gida kawai" "Na ji ba za a gaya masa ba, amma sai ka zauna an kula da kai tukuna". Madaki hankalinsa ya tashi, jin an kashe masa yaronsa na hannun damansa, a hannun wanda ba zai iya ɗaukar fansa ba, dan gaba da gabanta. Yana tsuma, suka tafi in da Dodo yake zama, aka ce sai dai su bishi asibiti, baya nan. Asibitin gwamanti ne, Amma amenity dodo ya biya aka kwantar da Al'amin. Madaki cikin girmamawa ya ce "Na amsa kira ranka ya daɗe". "Ka san wannan ai?" Dodo yayi maganar yana nuna masa Al'amin. "Na san shi" "Daga rana mai kamar irin ta yau, idan kai ko wani daga cikin yaranka, ya sake taɓa shi, ko tsoratar da shi, wallahi sai na ƙarar da tarihin mutum a bayan duniya. Bana shiga harkar ƙananan dabarku, amma aka kuma ratso unguwar nan, aka taɓa shi, wallahi sai na yi abun da ba a zata ba. Ka durƙusa ka bashi haƙuri a kan cin zarafin da ka saka aka yi masa, ka sanya karnuka suka yi masa illa, yana ɗan adam ba dabba ba, sauran abun da ka yi masa kuma kai da shi ne". Madaki ya kalli Dodo ya ce "Ni zan bashi haƙurin?" Wani wawan mari, dodo ya ɗauke madaki da shi, da sai da ya kife ƙasa, "Ka shiga hankalinka, ka san da wa ka ke magana kuwa? Har ka mutu ba zaka yi iskancin da nayi ba, shekarata goma a ƙiri-ƙirin lagos, ba wani ɗan iskan da ban gani ba, ko ban sani ba, ka bashi haƙuri, ko na ciyar da macizaina namanka" Madaki ya kalli Al'amin, shi ma ya kalleshi, ya kalli dodo sannan ya ce "Ka yi haƙuri, bisa abun da na saka aka yi maka da karnuka". Al'amin ya ce "Ko ka bani haƙuri ko baka bani ba, gaba da ni da kai sai ranar da na rama zubar da jinin ɗan uwana da ka yi" sai da duk suka kalli Al'amin, Al'amin ba dai taurin zuciya ba. Madaki ya fice a muzance, a gaban yaransa aka saka ya bawa Al'amin haƙuri, an wulaƙanta shi ƙarshen wulaƙanci, dan haka ya ƙullaci abun a ransa. Al'amin har ya kwana huɗu a asibiti, Abbu bai neme shi ba, kullum abincinsa mai rai da lafiya yake samu ya ci, ga dodo shi ma kullum sai ya zo duba shi, ya yi ta yi wa Al'amin hira, har yaransa suka fara mamakinsa, dan Al'amin ba wani sakin jiki yake da shi sosai ba. "Al'amin da gaske kana son ka rama abun da madaki yayi maka?" Al'amin ya ce "Eh" "Tunani mai kyau, amma ka sani shi ƙarfe dole sai da ɗan uwansa ƙarfe, yanzu an sallameka, mu je mu kai ka gida, sai ka din ga zuwa dressing, na biya kuɗin dressing ɗinka, duk abun da ka ke buƙata zan baka adress ɗina, a nan cikin unguwar, ka je ka same ni" Al'amin ya jinjina kai ya ce "Na gode sosai" ya dafa kafaɗarsa ya ce "Kar ka damu Aminullahi" Da ya koma gida, babu wanda ya tambayi ina yaje, tsawon kwanakin nan, ga jikinsa duk raunuka,  amma babu wanda ya tambayi ya yake, sai ƙanwarsa shahida da suke uba ɗaya. Tun da dodo yayi wa madaki iyaka da Al'amin, ya samu sassauci, ya cigaba da sabgoginsa, bai kuma sake bi ta kan dodo ba. Da ƙyar ya samu aiki a wurin wani mai shayi, yake yi masa wanke-wanke da abun da ba a rasa ba, idan ba ya nan, da shi da ƙanin mai shayin ne suke riƙe wurin, hakan ya sanya ya fara rage damuwa da halin da yake ciki. Sai dai ƙanin mai shayin ya nemi da su haɗa kai da Al'amin, su ɗan din ga ɗaukar wani abu, Al'amin ya ce ba zai yi ba, ba a jima ba, yaron ya yi wa Al'amin sharri wai yana ɗebar masa kuɗi, kuɗi kusan dubu talatin, mai shayi ya kai Al'amin wurin 'yan sanda aka daka aka yi rarrashin ya ce shi bai ɗauka ba, ba kuma zai amsa yayi ba. Aka yi ta kai ruwa rana, da ƙyar case ya mutu, bayan ya shafe kwanaki a hannun 'yan sanda. Yamma liƙis, ya je ya samu ƙanin Habu mai shayi, har rumfar mai shayi, ya karya shi a hannun dama, aka kuma cafke shi zuwa wurin hukuma, aka nemi Abbu, amma ya ce ba ruwansa, tun da kangarewa ya ɗauka. Ɗaya daga cikin matasan da suke yi wa dodo aiki, wato Walid, shi ya gaya masa halin da ake ciki. Da kansa yaje station ya karɓo Al'amin. Ya saka shi a gaba, yana yi masa tambayoyi, a kan dalilin da ya sa, ya aikata abun da yayi. Ya kwashe komai ya gaya masa. Dodo ya ce "To daga yau, kar ka sake zuwa ka nemi wata sana'a, duk abun da ba ka da shi, ka zo na baka. Na fuskanci tsohonka baya yinka, ni kuma ehhh kawai ka kwanata mini a rai, tausayi kake bani, kana rayuwa da kai da wanda aka bugoku cikin samfurin jini ɗaya, an ɗaye maka shi, ta ƙarfin tsiya. Amma ba komai, zaka rama ne" Tun daga lokacin Al'amin ya zama yaron dodo, wurinsa yake zuwa ya karɓi kuɗin abinci, ya biya masa kuɗin registration, ya mayar da shi makaranta ya cigaba da HND, dama shekarunsa ba su kai shiga University ba, shiyasa ya fara zuwa poly. Dodo harkar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi yake yi, babban distributor ne, har garuruwa yake rarrabawa kaya. Bai damu da harkar daba ba, sai wannan sana'ar, Abbu bai taɓa tuhumar ya aka yi Al'amin ya koma makaranta ba, wace sana'ar ya fara duk bai tuhume shi ba. Dodo yana da manyan yara da matasa, ciki har da sa'an Al'amin mai suna Walid. Sai dai Walid ya tsani Al'amin ganin yana neman ƙwace masa fada a wurin dodo babban sarki. Ko aike babu wanda ya isa ya aiki Al'amin, dodo ne kawai yake sa shi ko ya hana shi, haka zai zauna a cikin su, su yi ta shaye-shaye suna ƙuƙƙula kayan maye, amma ba ruwansa da su, ko sigari bai taɓa gwada sha ba. Idan yayi dare a yawonsa, sai ya tafi gidan dodo, yayi kwanansa, dodo har safarar makamai yake yi, babban criminal sosai da sosai. Komai Aminullahi, komai Aminullahi, lokaci lokaci, ya kan tuntuɓi Al'amin, ko zai iya yafe wa madaki, amma ya ce har abada, har sai ya rama abun da yayi masa ya kan yi murmushi ya ce "Aminullahi kenan, in dai zaka zauna a haka, ba ka shirya ɗaukar fansa ba, ƙarfe dole sai da ɗan uwansa ƙarfe, roba ba ta tasiri a kan ƙarfe" baya gane mai dodo yake nufi, dan haka sai dai ya bi shi da to Al'amin ya ce masa dan Allah ya samo masa sana'a, ko wace iri ce zai din ga yi. Dodo ya ce masa zai duba. Duk abun da Al'amin zai yi, dodo bai yadda yaransa su yi masa wani abu na horo ko cutarwa ba, hatta kaya idan Al'amin ya cire, sai ya ce Walid ya wanke masa, wanda kan zuwan Al'amin shi ne na gaban goshi. Sannu a hankali, ya fara aiken Al'amin kai kayan shaye-shaye wasu wuraren, cikin dare idan motar kaya ta isao, haka zai ɗauke shi, su tafi su karɓo kaya. Wataran ya aike shi, hukumar hana sha da fataucin, suka kama shi, aka din ga tuhumar Al'amin, ya ƙi faɗan wanda ya aike shi da kayan, sai da aka kwana biyu ana nemansa, hankalin dodo ya tashi, aka bincika aka gano masa shi a hannun hukuma. Ya je ya karɓo Al'amin, sannan ya ce "A bashi kayan da aka ƙwace ayi musu kuɗi zai saya, idan suna da wasu ma a haɗa masa ya saya. Kuma hakan aka yi. Ya yi ta yi wa Al'amin faɗa, a kan dan me, ya zauna a hannunsu, bai saka an neme shi, ya fito da shi ba?. Ta kai ta kawo, Dodo yana tafiya da Al'amin wurin 'yan siyasa, dan a nan ne suka haɗu da Indabo, a lokacin baya shan komai. Duk da wannan abubuwan da suke wakana, Al'amin yana zuwa gida, ya ga Abbu, ko da kuwa zai yi masa faɗa ya kore shi, yana zuwa ya ganshi. Yaran dodo sun sha attempting koya masa shaye-shaye, amma ya ƙi, tun Walid yana jin haushin Al'amin, har ya haƙura, manyan yaran dodo suka saka masa mai zamani, ya kori gwamantin Walid dan haka idan yana son zaman lafiya ya kiyayi mai zamani" Dodo ya din ga dariya, ya ce "Kuma zamanin Aminullahi dogo ne a wurin dodo ba, bana tunanin akwai wanda zai ture gwamantin sa a wurina, dan mai dogon zamani dan haka mai laya" yayi maganar yana kallon Walid. Aka haɗa baki aka ce "Ka kiyayi mai zamani" suka yi abun da sigar raha. Al'amin ya je gida, domin ganin Abbu, amma ya tarar baya nan, Rahila kuma tayi baƙi, ya shiga kitchen ya ga an yi uban abinci, ya kwaso fulasan yayi gareji da su, ya zauna ya hau ci, duk da ya san na baƙin ne. Yana cikin ci, sai ga wata 'yar yarinya ba ta fi shekaru biyu ba, ta zo in da yake tana kallonsa, ta tsuguna ta saka hannu a kwanon, tana tsintar abincin tana ci. Ya kalleta, sai ya tuna jaririyar ummi da ta rasu, yanzu ga shi duk su ukun babu su. Sai ya din ga bata abincin a baki, amma hakan bai hanata saka hannu a kwanon miya ba, haushi ya kama shi, kamar ya kwaɗe ta, ya kama rigarta yana goge mata hannun, kawai ya ji salatin Rahila. Ya ɗaga kai ya kalleta ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, na shiga uku jama'a ku taimake ni, zai lalata 'yar mutane, Allah ya sa ba yi mata komai ba" Sai yayi saroro yana kallonta, ya rasa gane mai take nufi, wanda ta yi hakan ne, dan huce takaicin tozarcin da yayi mata, na cinye abincin baƙi. Shahida ta ce "Mama wanke wanke nake yi, ina hango su ba abun da yayi mata, abinci kawai yake bata" "Ƙarya ne rufe mini baki dan ubanki, ke kin taɓa ganinsa yana ɗaukar yara ne, balle ba da abinci a baki, ni na ga abun da na gani" dama 'yar ta maƙwabta ce, uwatta ta kawota ta fita. Ta tara wa Al'amin jama'a, wai ya saka wa yarinyar hannu a wando, da idonta abun da ta gani kenan. Duk dakiya da dauriyar Al'amin, jikinsa ya hau rawa, ya kasa ko motsi daga wurin, mutane suka taru a garejin gidan, Abbu dama sallar la'asar ya fita, a masallacin yana lazumi aka je aka kirawo shi. Cikin tashin hankali ya danƙo Al'amin, ya kwaɗa masa mari ya ce "Me ka yi wa 'yar mutane? Al'amin lalacewar taka har ta kai ga haka? Ni zaka zubarwa mutunci a idon duniya" Shahida tana kuka za ta yi magana, Rahila ta hanata, wata mata ta cire pampers ɗin yarinyar ta duba ta, ta ce "Wannan yarinyar fa babu abun da aka yi mata, lafiyarta ƙalau da ya taɓata ma, ba za a ganta a haka ba" Al'amin ya ƙwace rigarsa daga hannun Abbu, ya fice, yana jin zuciyarsa zata tarwatse, bai zarce ko ina ba, sai gidan dodo, suna ganin sa suka din ga tambayar sa, menene saboda yadda idonsa ya yi jawur, amma ya yi shiru ya ƙi kula kowa. Walid ya kira dodo a waya, ya sanar masa ga mai zamani ya zo, cikin ɓacin rai da tashin hankali. Ba a ɗauki lokaci ba, sai gashi, ya ce "Waye ya taɓa zuciyar magajin dodo, wa ya taɓa mini Aminullahi?" "Al'amin ya ƙi magana sai huci da ajiyar zuciya, ga wani gumi da yake yi" Dodo ya ce "Walid" "Allah ya taimaki babban sarki" "Narka jan tablet, ka bani" Walid ya narka ya bashi, ya miƙa wa Al'amin. Ba tunanin komai, ya karɓa ya shanye ya ajiye kofin, wani zuuuuu ya fara ji a kansa, ya fara ganin hazo-hazo, a hankali ya fara ganinsu bibbiyu, daga haka bai sake sanin abun da ya faru ba, sai sha biyun dare ya farka. Yayi sallolinsa, ya ci abinci, dodo ya ce "Magajin dodo, ba zan takuraka na ji menene ba, amma ya ka ke ji yanzu damuwar ta tafi gaba ɗaya?" Al'amin ya girgiza kai alamar a'a. "Duk wannan dogon zangon da ka yi? Bari na baka wani haɗin" Ya naɗa masa wiwi, ya kunna ya bashi, sai dai zuƙa ɗaya Al'amin ya hau tari, kamar zai shiɗe ya ce "Ƙara gwadawa, ba zaka yi ba" ya din ga zuƙa a hankali, tun yana tarin har ya daina. Ayshercool 08081012143 A din ga yi, ana sauke hakki ₦500 0009450228 Aisha Adam jaiz bank 37 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Tun daga lokacin, Al'amin ya fara shaye-shaye. Shiga layinsu ya gagare shi, saboda tsananin kunyar abun da Rahila ta yi masa na sharri. Sai da ya shafe wata guda bai sake takawa gidan su ba, sai dai kewar Abbu ta din ga damunsa, da asuba ya tafi masallacin da Abbu yake salla, ya yi sallar asuba a waje, ya jira ya fito, Abbu yana tafe ya ji kamar ana bin sa a baya, ya tsaya ya waiwaya, duk da gari bai gama yin haske ba, da sauran duhu, amma hakan bai hana abbu gane Al'amin ba. Ya tsaya, jiki a sanyaye ya ƙaraso, Al'amin ya risuna ya ce "Ina kwana" "Kai daga ina? Ina ka tafi tsawon kwanakin nan? Duk yawonka ba ka wuce kwanaki kaɗan, amma ban sake saka ka a idona ba" kallon Abbu yayi, yana tunanin da ma yana jin wani abu idan bai saka shi a idonsa ba?. "Ina nan" Abbu ya ce "Kana can kana shashanci, gaishe ni ma ba zaka iya zuwa ka yi ba ko?" Ya ce "Korata ka ke idan na zo" "Ba dole in kore ka ba? Tun da kai a rayuwarka ba ka gaya wa kanka gaskiya, kuma duk in da ka zauna sai an yi faɗa da kai. Ka yi salla ne?" Al'amin ya jinjina kai. "To wuce mu tafi" yayi maganar yana nuna masa hanya, sai Al'amin yayi ajiyar zuciya, tare da tuna masa baya, da yake ɗora shi a wuyansa idan suka dawo daga masallaci, har tsere suke yi da Abbu, duk yadda Abbu yake ji da shi, yanzu ya zama tarihi. Yana tuna abun da ya faru ƙarshe, sharrin da Rahila ta yi masa, sai ransa ya ɓaci, ya ƙi shiga layin ya tsaya. Abbu ya waiwayo ya ce "Ya ka tsaya kuma?" "Tafiya zan yi" "Zuwa gidan uban wa?" Al'amin ya ce "Da wani idon zan kalli sauran mutanen layin, bayan ga sharrin da aka yi mini, idan na ga matar nan, zan iya kasheta, sai anjima kawai na tafi, dama ganinka nake son na yi, tun da kana lafiya Allah ya ƙara lafiya" ya juya ya tafi, Abbu ya tsaya yana kallon Al'amin har ya ɓace wa ganinsa. Ko da ya koma gidan da suke, walid ya fuskanci Al'amin yana cikin damuwa, yayi masa tayin sigari, ya girgiza masa kai, can ya ce "Walid" Ya amsa da "Na'am" "Dan Allah ya aka yi ka fara Shaye-shaye?" Walid ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Wan babana ne ya cinye mini gado, nake ta wahala ina fama da rayuwa, matsin rayuwa ya isheni, kuma shi ba tallafa mini yake yi ba, kawai na fara dafar kan kayan mutane, kuma da nasa na fara, aka kama ni aka kulle, rodi ma na sata lokacin, aka ɗaure ni watanni shida, da aka kai ni prison ban saba ba, nake ta kuka saboda wahala, a can na haɗu da mai gida, sarki dodo, ya din ga kula da ni, bayan ya fita ya dawo ya biya mini tarar aka yanke mini, sake ni, kawai ya cigaba da kula da ni" "Ina mamanka?" Walid ya ce "Taɓ tana can tana fama da rayuwarta, kinko ya kanannaɗe rayuwarta, wannan tsohon auran wan baban namu, ya tattare gadonmu ya cinye, Sakandire kawai nayi, ita ma ba ganewa nake yi ba da kyar na kai. Tana fama da kula da ƙannena, ga bata da cikakkiyar lafiya, ni kuma bana iya tallafa mata, har gara yanzu mai gida ya kan bani kuɗi ya ce na je na gaishe ta" Al'amin ya jinjina kai ya ce "Ka cigaba da kula da ita, dan duk ranar da ka rasata, za ka yi kuka, kuma kar ka bari ta san irin rayuwar da ka ke yi" "Na nawa kuma, ai wancan tsohon munafukin tuni ya gaya mata, tana yi mini nasiha sosai da addu'a, ba ta taɓa fushi da ni ba" Daga haka Al'amin yayi shiru, yana cigaba da tunani. Da sannu Al'amin ya zama gawurtaccen mashayi, duk in da dodo za shi, da Al'amin. Ta kai ta kawo har kudancin Najeriya yake tafiya da Al'amin, ba fatauci ba, har wuraren sarrafa miyagun ƙwayoyi Al'amin ya sani, har manyan mutane a ƙasar nan da suke ta'amalli da su da kasuwancin su ya sani. Ya haɗa Al'amin da wani inyamuri, ya ƙara gogar da shi a kan harkar na'ura mai ƙwaƙwalwa, yadda ake amfani da ita a aikata laifuka daban-daban, suka sake danganawa da wani bature, ya ƙara koyar da Al'amin sarrafa computer wurin yin laifuka. Ya zamana kasuwancin miyagun ƙwayoyi, na ƙasashen da suke maƙwabtaka da Nigeria, Al'amin ke tafiyar da kasuwancin su ta online. Bai tsaya a nan ba, har cikin manyan 'yan fashi, dodo yake shiga da Al'amin. Dodo ba ya fashi da makami, amma zama a gidajen gyaran hali daban-daban ya sanya ya san masu laifuka kala-kala da yadda ake aikata su, bai fiye harkar daba ba, yafi gane wa safarar ƙwayoyi da makamai. Idan aka cewa Al'amin magajin dodo, sai dodo ya ce "Wannan dodon, da sauran imani a ransa, ɗan ƙaramin dodo ne, ba zai iya zama kamar ni ba, sonake ya horu, yadda zai iya tunkarar kowane ƙalubale, ciki har da babban burinsa na son ganin bayan madaki, dan kuwa madakin ma ya ƙwafe shi a rai, na cewar sai ya ga bayansa, tun da na saka ya sanya gwiwar sa a ƙasa wurin bashi haƙuri". Duk wani sirri na dodo, babu wanda Al'amin bai sani ba, kallon abu dodo yayi Al'amin ya san me yake nufi. Kai tsaye ya kan tura Al'amin wurin indabo, a lokacin yana fafutukar neman kujerar ɗan majalisa, sai dai wasu lokutan baya son dodo ya aika masa Al'amin, dan idan yayi masa abun da bai yi masa ba, tafiyar sa yake ya ƙyale shi, ba ya jure cin zarafi ko wulaƙanci, komai ƙanƙantarsa, ya yaɓawa indabo baƙar magana ya ƙara gaba, duk ba abu ne mai wahala a wurin Al'amin ba, Indabo ya kai wa dodo ƙarar Al'amin. Amma ya ce "Ina nema masa afuwa, ka riƙe Al'amin yaro ne mai amana, kuma duk cikin yarana babu wanda zai iya yi maka aikin da ka ke so bayan shi, yaro ne mai amana sosai da sosai, kuma ba shi da surutu, hakazalika yayi hannun riga da tsoro. Dodo ne ya nuna masa makamai kala-kala samfurin wuƙaƙe, da in da in ka sakawa mutum zaka kashe shi, da wanda za ka yi masa illa. Dodo yana yawan faɗar, Son da yake yi wa Al'amin daga Allah ne, bai taɓa son abu sosai da yake jin sa a ransa kamar shi ba. Ya san son da yake yi masa, ba zai kai na ɗa da uba ba, dan haka ya din ga mamakin yadda aka yi, mahaifin Al'amin ya wofantar da shi, duk da soyayya irin ta ɗa da uba. Ba yadda bai yi da Al'amin ya ɗora karatu ba ya ƙi. Ya ce "Aminullahi, harakar daba da shaye-shaye ba abune da nake yi maka fatan ka ɗore a kai ba, yakamata ka koma makaranta. Al'amin ya ce "Ni ma ba na fatan na ɗore, ina ɗaukar fansar abun da madaki yayi mini zan bar daba". Ya dafa kafaɗarsa ya ce "Ina maka fatan hakan, sai dai haryanzu ba ka kai ƙarfin da zaka tunkari yaron nan ba, dan kuwa shi har da tsafi yake yi, kai kuma na san komai za a yi maka, ba zaka yi tsafi ba, amma ba a shiga dawa dan ƙarya, ko na kare kai, zan nema maka". Duk da an ɗauki lokaci, yaran madaki ba su shiga unguwar su Al'amin ba, sai rana tsaka, suka shigo unguwar neman faɗa, a karon farko Al'amin ya ɗauki makami, jikinsa na wata irin tsuma, zuciyarsa na tafasa, wanda hakan ya faru ne a sakamakon abubuwan da yake ta'amalli da su. Dan shaye-shaye nasa, kala-kala ne, kowanne akwai lokacin amfaninsa. Idan wani aiki yake son yi, ba ya son gajiya da wuri, sai ya banki wiwi sai ya daɗe yana abun da yake so, ba tare da ya gaji ba. Idan kuwa rashin mutunci yake son yi, haka zai yi mata haɗe-haɗe na mussaman, haka ma idan so yake ya bugu. Bai fiye ta'amalli da ƙwaya sosai ba, ya fi ƙarfi ga wiwin. Ya je ya samu yaran, kan mai uwa da wabi, yayi musu ɓarna, sannan ya taka har dabar madakin, ya yi masa warning, "Ka gargaɗai karnukanka, a kan shigar mini area su nemi faɗa, idan ba haka ba, kan babban karen zan zo, na yi masa takunkumi, yadda haushi ma sai ya gagare shi" Madaki tun da dodo ya sanya ya bawa Al'amin haƙuri, ba su sake arangama ba, kusan shekara biyu, sai a wannan lokacin, sai da gabansa ya faɗi, saboda yadda kamannin Al'amin suka juye, ƙarara alamun shaye-shaye suka bayyana a tare da shi, yadda ya sake zuwar masa kai tsaye ba tsoro ko fargaba, ya sanya shi gane kuskuren da ya yi na barin Al'amin a raye. Tun da Al'amin yake tare da dodo, bai taɓa rashin kuɗi ba, kuɗi yake kamawa manya da ƙanana, kuma bai taɓa ci wa dodo amana ba. Har a cikin ma'aikata, ana samun ɓata gari waɗanda suke sayar wa dodo kayan maye, idan sun kama, duk wani salo na yadda ake sayar da kayan, ba tare da an gane ba, Al'amin ya goge, haka idan kana ta'amalli da su, kallo ɗaya zai yi maka ya gane. Yan kwamutin unguwa, suka kai ƙarar Al'amin wurin hukuma, a kan yana tayar musu da tarzoma, ba tare da la'akari da yaran da suke rashin jin tun kafin ya fara ba. Dodo ya je ya samu shugaban 'yan vigilant, ya ce masa "Wallahi duk wanda ya sake ɗaukar ƙafa, ya kai ƙarar Aminullahi sai ya ci ubansa, lokacin da aka kashe ɗan uwansa ku nawa ku ka tashi ku ka je wurin jami'an tsaro domin ganin an ƙwatarwa yaron hakkinsa, saboda ba yaranku aka kashe ba. Lokacin da yake ragaita ba shi da sana'a, mutum nawa ne suka mayar da shi makaranta? Ko suka bashi sana'a, dan mahaifinsa ya wofantar da shi, kuna 'yan unguwa ba ku ga dacewar ku nusar da shi kuskuren sa ba? Ai duk society da suka yi watsi da yaran su irin su Aminullahi muna nan muna jiran su, mu zamu karɓe su, mu mayar da su abun da ya dace. Gargaɗi nake yi, ni dai an san ba zan kamu ba, to haka Al'amin ma, ko bayan raina, ina da masu fito mini da shi idan ya shiga cakwakiya. Ku shirya Al'amin bai fara yi muku rashin ji ba tukuna" Ƴan unguwa suka rasa abun yi, yaransu da suke ƙanan rashin ji, suka fara bin Al'amin, yana ba su kayan wiwi suna sayarwa, yana ba su kuɗi, dama gashi da kyauta kuma ba shi da baƙin ciki. Duk yaran dodo, suna shakkar Al'amin, ko dan saboda masifar dodo idan aka taɓa shi, dama Al'amin ya fi yin faɗa da Walid, dodo ya kan ce masa Mai laya, ka kiyayi mai zamanin nan, idan ka ƙure shi, ba zan saka baki ba, idan ya tashi yi maka ɓarna ba. Su yi faɗa su yi daɗi. Tafiyar gaggawa ta kama dodo, zuwa kudancin Najeriya, sai dai ya ce wa Al'amin ya zauna, ya kula masa da harƙallarsa ta kano, ba zai tafi da shi ba. Abun da Al'amin bai taɓa yi ba, sai a wannan karon ya ce "Meyasa ba zaka tafi da ni ba?" "Aminullahi, tafiya ce mai hatsari, ka kula mana da harƙallarmu, sannan kar ka manta rules ɗin, a tafiyarmu babu BODMAS, idan ka ji wuta, ka wargaza komai ka ɓace" Al'amin ya jinjina kai ya ce "Allah ya taimaki sarki babban dodo" "Na gode, Allah ya ja zamaninka, zuwa in da ba ka zata ba, a cigaba da riƙe amana Aminullahi" haka nan Al'amin ya ji baya son dodo ya tafi. Kwana uku da tafiyar Dodo, suna zazzaune, suna shan sigari, aka jefo wata jaka ta katanga. Walid ya ɗaukko jakar, wasu daga cikin yaran wurin, suka fita da gudun tsiya, suna neman wanda ya jefo jakar, ba su ga wanda ya jefo ba. Al'amin ya ja jakar ya buɗe, kawai yayi tozali da kayan dodo a ciki, face-face da jini, har da takalminsa. Cikin ƙaraji Al'amin ya ce "Nooooo" ya tashi jikinsa yana tsuma ya girgiza kai ya ce "Impossible, ba zai yiwu ba, sarki yana raye, raina mana hankali kawai ake yi" Walid ya riƙe Al'amin ya ce "Al'amin ka nutsu mana, musulmai ne mu, idan ba a kashe sarki ba, babu yadda za ayi a ciro kayans jina-jina a kawo mana". Al'amin ya fara neman ya fita hayyacinsa, Walid suka danne shi, suka shaƙa masa wani abu, jikinsa ya saki ya hau bacci. Al'amin ya razana, ya shiga tashin hankali, ya ɗimauce sosai da sosai, da mutuwar dodo, ba zai manta gudunmuwar da ya bashi ba, duk da ba ta arziki ba ce ba, Al'amin kamar zai zare. Duk wata hanya da zai bi ya gano wanda ya kashe dodo, ya rasa, damuwa ta ƙara yi masa yawa. Ya ɗaukko makaman da ya saka aka ƙera masa, sweazland, Russia da kuma iraƙi, ya zuba musu ido, bai taɓa zaton ya shaƙu da shi haka ba. Mussman madaki ya zo ya sami Al'amin, yana ƙyaƙyata masa dariya, wai garkuwar da fake a bayanta, an samu wani gwanin saitin ya rusata, yanzu zai koma Al'amin ɗin sa matsoraci na ainihi. Sai dai cikin sa'a, Al'amin yana tare da sweazland, dan haka madaki ya fara yi wa rauni da ita ya ce "Dan an fasa garkuwata, ba ya nufin zaka cim mini,  *Ƙarfen cikin wuta nake* na fi ƙarfin ɗauka da hannu, ko da mariƙin roba, daga yau ka rubuta ka ajiye, ɗaya ya riski ajalinsa ne kawai zai kawo ƙarshen gabata da kai". Madaki ya kalli cinyarsa da ke jini ya ce "Meyasa ba ka kawo ƙarshen gabar yanzu ba, ka kashe ni?" "Saboda na fika sanin waye kai, akwai lokacin da ya dace da hakan". Yaran dodo, sun so Al'amin ya gaji harƙallar dodo, ba ita ba har manyan hada-hadarsa da manyan mutane. Amma Al'amin yaƙi, ya ce baya buƙatar duk wani abu da zai din ga tuna masa da dodo, kuma zai yi abun da zai Allah zai gafarta masa, ba ɗorar da laifukansa a bayan ƙasa ba. Da yawa sun so su ya basu sirrikan dodo, su cigaba da sana'arsa, amma Al'amin ya ƙi, ƙarshe ma suka bar wannan gidan gaba ɗaya, ya je ya kafa masa sansanin. Walid suna zuwa da Al'amin duba mahaifiyarsa, da ciwon Cancer ya kama, aka kwantar da ita a asibiti, kullum cikin neman jini ake, duk wani kuɗi na Al'amin, sai da ya ƙare a wurin kula da mahaifiyar Walid. Liti dama shi isaknci ne da abokai, suka saka ya lalace, dan har waje babansa ya kai shi yin karatu, bai koyo komai ba sai shashanci ya dawo. Kasancewar jinin Al'amin da na babar Walid iri ɗaya ne, ya bayar da jininsa sosai an saka mata, kullum cikin Kwantar wa da Walid hankali yake, tare da bashi tabbacin zata warke. Har zariya suke kaita Asibiti gashi, amma cikin ikon Allah ta koma ga Allah, abun nan da Al'amin ya yi wa walid, ya sanya ya sanya duk abun da zai yi masa baya fushi da shi, ko yayi sai ya huce. Suka koma ƙaramar harƙallar sayar da wiwi, idan kuma aikin ƙarfi ya samu su yi. Al'amin ya numfasa sannan ya ce "Ban kuma taɓa kashe kowa ba, duk rashin ji na, wanda ki ka ganni da shi, liti ne, yaran madaki suka soka masa wuƙa, kar ki sake cewa na yi kisan kai". Jauhar wani irin kuka take man ban tausayi, rayuwar Al'amin akwai tarin ƙalubale, sai ta ga ita tata rayuwar nafila ce. "Ki yi haƙuri, da yawan furta miki zan sake ki da nake yi, baki cancanci mutum mai tarin laifuka irina ba, wallahi ba zan iya yafewa madaki ba, da shi da wanda suka kashe dodo. Ban yi miki alƙawarin daina abun da nake nan kusa ba, binciken da na ƙara yi akan ki, na fuskanci kusan ƙalubale ɗaya muka fuskanta, dan na san duk wani abun alkhairi wannan shegiyar matar ba zata bari ya raɓe ni ba, dan haka na yi zaton ta shirya mini wata maƙarƙashiyar ne, dan haka ta aura mini ke, ashe wai wani mai kuɗi zaki aura, suka hana ita da wannan banzar matar ta gidanku, ban manta lokacin da take zuwa gidanmu ba ita ma. Haryanzu a shirye nake, mu rabu ki auri mutumin kirki, baki dace da ni da rayuwata ba, rayuwata ta riga ta gurɓace, kullum kina cikin tashin hankali bai kamata ba, duk a sanadina. Dama kin ga ke kalar matan masu kuɗi ce, in da zaki huta a kula da ke sosai. Ni kuma na gurgura na ƙarasa rayuwata" Jikinta na rawa, ta toshe masa baki, ta kalleshi, hawaye wani na bin wani a fuskarta, amma ta kasa magana ta cigaba da sheshsheƙar kuka iya ƙarfin ta. Ya sauke hannunta daga bakinsa ya ce "Lafiya kuwa? Wannan kukan fa?" "Zan zauna da kai a haka, na san wataran zaka daina, a lokacin da raɗaɗin kaɗaici da damuwar da ka ke ciki suka barka, a lokacin da ka fahimci wani zaluncin idan an yi maka wata shari'ar sai a lahira, ba zaka iya ɗaukar wa kanka mtaki ba. Zan zauna da kai har zuwa lokacin da komai zai zama tarihi. Ni ba zama da mai kuɗi ne damuwata ba, kwanciyar hankali nake so, in da za a ga mutuncina a kula da ni, dama miji nagari nake fata ba mai kuɗi ba". Ya lumshe idonsa ya buɗe ya ce "To ni na garin ne?" Ta jinjina masa kai alamar eh. Murmushi ya yi ya ce "Tashi ki je ki kwanta, ɗaya da rabi yanzu. Ba zan manta ƙoƙarin ki a kaina ba, kina cikin mutane ma su muhimmanci da ba zan manta da su ba" da ta kalleshi, sai ta cigaba da zubar da hawaye, wani irin tausayin sa na ratsa zuciyar ta. Ya gyara pillow zai kwanta, ya kalli yadda take ta kuka, ya ce "Har mamki ki ke bani, yadda ki ke taƙarƙarewa ki yi ta kuka, ni fa da wayona, zan iya ƙirga sau nawa na yi kuka". Yayi maganar yana kwanciya amma ta cigaba da zama a wurin. "Idan ki ka bari na rufe ki a ɗakin nan, akwai ƙura" ta kalle shi ya ce "Ban taɓa ɗaga sweazland na fito da harshe, ba ta sha jini ba, sai a wannan karon da ki ka hana ni, ko ki tafi ko in sha naki jinin in huce". Wato shi gaba ɗaya labarin da ya bata ma, ko a jikinsa. Sai da ta gama koke-kokenta, sannan ta tashi ta fita daga ɗakin. Ba ta kwanta da wuri ba, ta daɗe tana salloli, da karatun Alqur'ani, a kan Allah ya shirya Al'amin, ya sanya tarayyar ta da shi, ta zama sanadin shiriyarsa. Sai da tayi sallar asuba, sannan ta kwanta, dan haka wani irin nannauyan bacci ya ɗauke ta. Sama-sama ta ji muryar Al'amin, yana faɗa da boti, ya zo tashinta yana jin yunwa, ya ga boti ya lafe a jikinta, shi ma yana tashi. Ya danƙo shi ya jefa ƙasa ya ce "Ware ka bar nan wurin dan ubanka" Boti ya tsaya, yana kallon Al'amin yana kuka. Al'amin ya mayar da idonsa kanta, bacci take sosai, shi kuma yunwa ta ishe shi, dan yayi shaye-shaye. Dukan katifar gadon yake yi a hankali, ta motsa kaɗan ta cigaba da bacci. Yaye bargon yayi gaba ɗaya, daga ita sai vest da gajeren wando, a razane ta tashi zaune tana kare jikinta. Ya riƙe bargon ya ce "Ki na ji na ki ka yi mini shiru? Ina son na karya na sha magani, kin ɗauki wancan abun kin kwanta kina bacci da shi". Cikin muryar bacci, mai haɗe da tsoro, ta ce "Na ji, amma ka bani bargon zan fito yanzu". Ya ce "In tafi ki cigaba da baccin, tashi mu je" To ka je ka jira ni, zan saka kaya. Taɓe baki ya yi ya ce "Da kin kwantar da hankalinki, ba na jin komai, ba abun da zan yi miki" ya miƙe yana ajiye mata bargon ta, ya danƙo kan boti ya yi waje da shi. A jejjere ta din ga ajiyar zuciya, tana maimaita maganarsa shi ba ya jin komai. Da ta fito kasa haɗa ido tayi da shi, ya kwanta ruf da ciki saboda raunin bayansa, yana jiran abinci. Bayan ya karya, ta ce "To wanka fa?" "Ba yanzu ba, gasa mini ciwon nan kai" Ta haɗo ruwan ɗumi, ta gasa masa, ciwon, tana yi yana raki, saboda yadda ya ga tana damuwa sosai, wai da zafi. Wayarsa ta fara ringing, ta hana shi ɗagawa, har ta katse, ta sake fara ringing, ta ɗaga ta ce "Assalamu alaikum, ba shi da lafiya bacci yake" "Ya jikin nasa?" Ta ce "Da sauƙi" "Masha Allah, ke ce matar ta sa? Al'amin ya karɓe wayar ya kasheta gaba ɗaya ya kalleta ya ce "Meyasa ki ka tsaya kina magana da wani?" "Na zata su yaya walid ne, yi haƙuri, amma yakamata ka kira shi ka ji, ko an sako shi" Al'amin ya haɗe ce "Wai ke kowa ma damuwa ki ke da shi ne?" "To ai gani nayi saboda mu ya shiga matsala, aka kama shi" "To ba ruwanki, da ni kawai zaki din ga damuwa" ta kwashe da dariya ta ce "To shugaba, in sha Allah. Juya in shafa maka man zafin a wurin" ya juya tana shafa masa a hankali, dan kar ya ji zafi. Wayarta ce ta fara ringing, ta ɗauka ta duba Ta ga lambar mama ce, ta ɗaga suka gaisa, ta ce "Yauwwa, dama kiranki na yi, ana ta shirin bikin hafsa, tun saura sati ɗaya biki yakamata ki dawo gida, akwai aikace-aikace da za ayi, saboda bikin. Ta ce "To shikenan mama, Allah ya kaimu lafiya" "Amin" ta kaste wayar. "Ba in da zaki" ya faɗa dai-dai lokacin da ta ajiye wayar. "Master meyasa, bikin Yaya hafsa ne fa" "Ko bikin wacece, ba zaki ba? Idan akwai mai neman dalili, sai a tuntuɓe ni". Jauhar ta ce "Master za su ga kamar wulaƙanci ne, ko baƙin ciki, ko ba zan yi satin ba, dan Allah ka bari na je bikin" Ya girgiza kai ya ce "No, bayan bikin kya je gidanta". Jauhar ta marairaice za ta yi masa magiya ya buga mata tsawa ya ce "Ina magana kina mayar mini, ba zaki je ba na ce" a razane ta ja da baya, ta sunkuyar da kai ta yi shiru, ya tashi ya bar mata falon. Yana ƙwafe da wayar da suka yi, aka ce ba zata iya sayen anko ba, yanzu kuma an ce ta zo ayi aiki, saboda baiwar su ce ita, ita kuma gaba ɗaya hakan bai dameta ba, wasu lokutan kamar ba ta da zuciya sam. Tun da Indabo ya ajiye wayar, yake jujjuyata yana jin yadda muryar jauhar, ke kai komo a cikin kwanyarsa, kana jin muryar ka san ta yarinya ce, haka kurum ya ji ya kwaɗaitu da son ganinta. Ayshercool 08081012143 38 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 da Indabo ya cigaba da jujjuya wayar yana kallonta. Sosai jauhar ta ji babu daɗi, hanata zuwa bikin da Al'amin yayi, ba ta san dalilin sa na yin hakan ba, kuma bai gaya mata ba, ba ta san me za ta ce wa su mama ba, su yarda da ita. Kuma yayi fuska, ya hau hura hanci yana wani basar da ita, dan ma kar ta ce zata yi fushi da maganar hanata zuwa bikin da yayi, shiyasa yayi sauri ya rigata fara fushin. Haka ta wuni, idan ta tuna abun sai ta ji ba daɗi, da duk in da za ta je, ba ruwansa, amma yau bikin 'yar uwatta, ya ce ba zata je ba, Al'amin kenan. Sai dai tayi iya ƙoƙarinta, ta danne fushinta, ba ta canza masa ba, amma yanayinta kallo ɗaya yayi mata ya gane, a cikin damuwa take, kuma ya san hakan yana da nasaba da hanata zuwa biki da yayi. Can gidansu amarya hafsa, ana ta rawar kai, an sha gyaran jiki, magungunan mata kuwa ba a magana, fatar nan ta ƙara ɗashewa, tayi fara ƙal kamar aljana. Sai hura hanci ake yi, za a auri mai kuɗi, mama kuma sai yi musu lumbu-lumbu, kamar tana tare da su a komai. Suka din ga karɓar kuɗi a wurin Alhaji mu'azzam kamar ba gobe. Shi kuma duk abun da suka nema, haka zai ba su. Zakiyya ta saka hafsa ta tambaye shi, wai a ina za su je honeymoon. Murmushi ya yi da ta tambaye shi ya ce "Hafsa yawon ƙasashen duniya har sai kin gaji, dai ƙasar da ki ke so zamu je" hakan ya ƙara fasa mata kai, ta din ga jin cewa ta gama dacewa. Al'amin ciwonsa ya fara warkewa, kasancewar ba shi da ƙan jiki, ga kulawa da Jauhar take yi da shi sosai da shan magani. Ta ɗaura aniyar, fara ɗora Al'amin a turbar tafiya masallaci kuma, ya din ga salla a cikin jama'a, kamar yadda Annabi Sallallahu alaihi Wasallam, ya kwaɗaitar da al'ummarsa, mussaman da ciwonsa ya kame, dan ya fara saka riga ya fita ma. Sai dai fa aikin ba na wasa bane ba, dan wasu lokutan idan ta tashe shi sallar, har a idar tana fama da shi bai tashi ba, mussman idan a cake yake, idan ta yi alwala kuwa ta zo tashinsa, ƙarshe sai ta ta alwalar ta karye, shi kuma bai yi ba. Sai dai ta tsananta addu'a da gaya wa Allah. "Ya Allah ga bawanka Al'amin, kai ka halicce shi, ka shirya wanda suka aikata laifuka fiye da nasa, Ubangiji Allah ka shirya mini shi. Allah ka sa ya shiryu a sanadin zamana da shi, Allah kar ka saka na ƙosa ko na gaji, Allah ka dubi niyyata ta son zama da shi da yin biyayyar aure kamar yadda ka umarta, Allah dan kunfayanunka ka shiryi wannan bawa naka" Duk in da jauhar ta ji Addu'ar biyan buƙata, irin su salatul haja, salla raka'a biyu, fatiha da sura, idan ta idar ta mayar da goshinta ƙasa, ta karanta la'ila ha illa ant subhanaka inni kunt mina zalimin. Ƙafa arba'in  da ɗaya, ba ta ɗagowa sai ta gaya wa Allah buƙatunta. Salatul tasbih, da sauran tasbihai haka take yi, tana yi wa Allah magiya da yin tawassuli da su, ta roƙi Allah ya shirya mata mijinta, ya haɗa kan su su zauna lafiya. Yau ta samu yayi sallar asuba ƙarfe shida saura da ƙyar, ta dawo dan ta saka shi yayi azkar, ta tarar har ya kunna sigari daga idar da sallar. Bai yi tsammanin za ta dawo ɗakin ba, kawai ya ji sallamarta ta shigo. Kamar yadda tayi tsammani, bai daina sha ba, kuma ya tsuke fuska. Ta ƙarasa gabansa ta zauna, ta zuba masa ido. "Kin san an hanaki shaƙar hayaƙi ko? Kin san ba cikakkiyar lafiya ce da ke ba" "Kai ma bai dace da kai ba, ina gaya maka ina son lafiyarka, su kan su masu kamfanin abar sun yi gargaɗi a kan haka, dan Allah ka ajiye magana zamu yi". Bai ajiye ba, yayi mata shiru yana cigaba da fesar da hayaƙin wani wurin daban. Tashi tayi ta zagaya, in da yake fesar da hayaƙin tana kallonsa. "Meye haka ne wai?" "Dan Allah ka ajiye mu yi magana" "Ina jinki ai" wani abu mai ɗaci ta haɗiye, kawai ta tashi ta bar masa ɗakin. Ta koma ɗakinta ta tsaya, kuka ya ƙwace mata, sai ta fara saito abubuwa, sai Al'amin ya sake burkice mata, tun da suka yi aure take yi masa addu'a, amma abun nasa sai a hankali. "Kul jauhar, kar ki yi saɓo, ko ki yi wa Allah butulci, Allah sami'ul alim ne, idan ka roƙa baka ga tasirin abun ba, lokacin ne bai yi ba, tun da shi ya ce mu roƙa zai amsa, kuma Allah ba ya sabon aiki' wata zuciyar ta gargaɗe ta. Istigfari ta cigaba da yi, ta nemi wuri ta zauna a tsakiyar gadonta, tana cigaba da tasbihi. Sai da gari yayi haske sosai, ta fita tana aiki, ya fito cikin takun ƙasaita, ya nemi wuri ya kame a kan kujera. Sai da ta kai zuciyarta, sanna ta iya ce masa "Ina kwana?" "Lafiya ƙalau" a ranta ta ce 'Ka yi laifi, kuma ka maze kana hura mini hanci, da ni ka ke zancen'. Ta ajiye masa karin kumallonsa, ta koma ɗakinsa, ta na gyarawa, yanzu ya rage watso mata kaya daga wardrobe, sai dai ya tara mata kayan wanki, a kan katifarsa. Tsayawa yayi a bakin ƙofa, yana kallonta. Yayi gyaran murya ya ce "Kin ce zamu yi magana, ta menene?" Ta kalleshi ta ce "Ka manta kawai" ta ƙarasa maganar tana kwaso kayan wankin za ta fita. Har ta gota shi, ya janyo ta kamar wata 'yar tsana, ya tsuke fuska ya ce "Gaya mini menene?" Ta sunkuyar da kanta, hawaye ya fara zubowa daga idonta, wani na bin wani. "Menene kuma yanzu?" Cikin rauni ta ce "Kai ne" "Na yi me?" "Kusan kullum sai ka sakani kuka mussaman kwanan nan, na ce dan Allah ka daina shan komai ka ƙi dainawa, haba master wane irin uba ka ke son ka zama idan Allah ya bamu zuriya? Ina son in ga ka daina shan komai ka daina abun da ka ke yi. Amma ƙir-ƙiri ɗazu ka ƙi daina sha". Ya ce "Ke, wai an gaya miki daina shaye-shaye kamar daina cin tuwo ne? Ina ƙoƙartawa fa, duk kin addaba mini, ina ji ina gani, asuba ina shan kara biyar zuwa sama, amma ɗazu uku kawai na sha amma ba kya gani, kuma yaushe na ganki, balle a tara wata zuriya? Shiyasa ma ban bari sun ƙaraso ba tukuna sai na gama abun da nake yi. yayi maganar yana basarwa. Wata irin kunya ta kama ta, jin abun da ya mayar da maganar. "Ki daina damuwa, ina ƙoƙari sosai, ba zan iya dainawa ba, sai na cika burina, mutum ɗaya kawai zan kashe, shikenan" Jauhar ta kalleshi ta ce "Kisa kuma? Ana ga ƙura kana ga yaƙi, idan an yi nan sai ka yi can" Dogon harshensa ya zaro mata, yayi wani irin murmushi, sai ta ga kamar ya canza gaba ɗaya, ya dafo kafaɗarta kamar ƙawarsa ya ce "Bar wankin, zan yi ki haɗo da naki ma, idan na gama zan yi gyaran kwatar layin nan, duk an bari ta cushe da shara, me zaki dafa mana da rana?" "Master ba ka da aiki sai zancen abinci ne?" "To idan ban yi zancen abinci ba zancenki zan yi babyn roba" "Saura ta katako, rana zata yi mini, ko wankin ka saɓa sai na yi mana ɗauraya" Al'amin ya ce "A'a ki yi aikin ki zan wanke" yayi maganar yana yi mata wani irin kallo tare da murmushi. Ita ma murmushin ta yi masa ta ce "Harshenka dogo ne, meyasa ka ke fito da harshe ne?" Ya ce "Rantsuwa ce, kowane specie ɗinmu, akwai irin ta su". Jauhar ta yi dariya ta ce "Wai specie kamar a biology?" "To in ce kowane ɗan daba?" Ta yi saurin girgiza kai ta ce "A'a ba na son wannan kalmar, babu daɗin ji" Ba tare da ta gane ba, yayi mata wayo, ta daina fushin da take yi, dan babban burinta ya kula ta, ya sakar mata fuska. Aka shiga satin bikin Hafsa, Anty Zakiyya ta kira Jauhar ta ce "Jauhar wai yaushe zaki zo ne? Ayyuka sun kacame, ko dai baƙin ciki ki ke yi da lamarin nan ne?" Jauhar ta ce "Haba Anty, ba haka bane wallahi. Kin ga maigidan ne ba ya jin daɗi, idan na taho babu mai kula da shi". "Kamar yaya? Au mijinki ya fi 'yar uwakki, kamar wani mijin kirki, da waye yake kula da shi idan ba shi da lafiyar?" "A'a Anty, ai miji duk in da yake miji ne, yana buƙatar kulawa ne, ba dan.... "Dalla yi mini shiru, har wani tinƙaho ki ke yi da wannan abun? Makakken ɗan wiwi. Ba tare da Anty ta sani ba, tuni ya karɓi wayar daga hannun jauhar, ya saka a kunnensa tana ta masifa "To ki zauna sai yadda yayi da ke, ai mutumin kirki mai kuɗi shi yake saka doka a bi, ba irin mijinki ba da har ki ke gaya mini wai ai miji miji ne ba". "Makakken ɗan wiwi yana godiya, kuma kun san da makakken ne, ku ka aura mata ni. Ni na hanata zuwa matata ba baiwa ba ce, ta zo ta yi muku bauta, ba zata zo ba, idan kun ga dama ku bar bikin kar ku yi" Jauhar tana girgiza masa kai, amma sai da ya gama maganar ya jefar da wayar. "Master, iyayena fa, ba a haka yakamata a gaya musu ba, da ka bi a hankali, na san yadda zan gaya musu". Al'amin ya ce "Kin san bani da tarbiyya, ban iya magana da manya ba" "A'a ba haka nake nufi ba" "Idan ma dai hakan ki ke nufi, idan kuma ban isa ba, ki shirya ki tafi " Jauhar ta ce "A'a ka ma isa, ai na fasa zuwan, amma ai ka yi mini alƙawarin zaka kai ni gidanta bayan bikin ko?" Tausayinta ne ya kama shi, ba dan haka ba da gidan hafsan ma ba zai bari ta je ba, amma ya tuna ɗan uwa duk in da yake daɗi ne da shi, kuma bai kamata ya hanata zuwa wurin 'yar uwatta ba, amma kamar ko a jikinsa ya ce "Zan yi shawara" Anty Zakiyya kuwa, sai da kayan cikinta suka yanutsa, saboda tashin hankali da ta ji muryar Al'amin a waya. Sai dai jauhar ta sha zagi a gidan, ana cewa baƙin ciki ne da hassada ya sanya ba zata zo ba. Yaya saifu ya ce 'm"Jauhara ba ta da irin wannan zuciyar, hankalinta na kan mijinta, wannan aure dai, in dai dan cin amana aka yi shi, ba in da zai je zai watse". A fusace Anty ta ce wa mama "Ki ja wa ɗanki kunne, kar ya sake aibata mini auren 'ya" An kai kwanaki huɗu ana events kala-kala na auren Hafsa, jauhar sai kallo da ta din ga yi, tana murmushi tare da jin babu daɗi rashin halartar auren yayarta, ga 'yan uwa da abokan arziki duk an taru. Ita ma ta ɗora hotunan, tana yi wa hafsan fatan alkhairi. Aka gama biki, aka kai hafsa gidanta, wanda suke haɗe da uwar gidansa, kowacce part ɗin ta daban. Aka yi sayen baki aka watse, ya tara su yayi musu nasiha, bayan Uwargidan ta fita, Alhaji mu'azzam ya ce "Bari na je na ɗan ƙara rarrashinta, na san tana cikin damuwa" haushi ya kama hafsa, dan a zatonta yana zumuɗinta, ba zai saurari uwar gidan ba. Sai dai har ɗaya na dare bai dawo ba, ta kira wayarsa a kashe, tun tana saka ran ya dawo, har ta gaji, bacci yayi awon gaba da ita. Da safe ma, ga yunwa ga gajiya, amma ba ta ganshi ba, sai sha ɗaya na safe. Ya ce "Jauhar am sorry please" ta kalle shi cikin takaici ta ce "Jauhar kuma?" "Afuwan Hafsat, wallahi madam ce nayi  ta faman rarrashinta, taƙi yin shiru kin san kishi babu daɗi, shiyasa na zauna da safen nan ma da ƙyar na fito, duk a cikin damuwa ta ke, yanzu haka kanta ciwo yake saboda kuka, ina ga da kaina zan fita nema mata magani" Tamkar hafsa ta zabga masa mari haka ta kalleshi ta ce "Ni bana buƙatar kulawarka kenan sai ita?" Ya ce "No ba haka bane ba? Ai ke sabuwa ce, sai ta fiki shiga damuwa, bari na je na sayo mata maganin na kai mata, na yi ordern abinci, idan ban dawo da wuri ba ki karya kawai. Abu kamar wasa, har wurin kwanaki uku, bai saurari hafsa ba, wai uwargidansa ba ta da lafiya, har ma ya ɗauki fushi da ita, wai ba ta je ta yi mata sannu ba, ta ɗauki waya tana kuka ta sanar da Anty, Hankalin Anty ya tashi, ta ce ta je ta dubata ɗin, za su sake shiri su ma. Baya nan hafsa ta shiga duba ta,  ta ce "Na ji an ce baki da lafiya, na zo duba ki" Ta ce "Ko ɗaya, lafiyata ras, kawai ina ƙoƙarin nuna miki ƙarfin ikon da nake da shi a cikin gidana da irin gangancin da ki ka aikata na shigo mini gida" Hafsa ta ce "Shigowar ai ita ce mai wuyar, tun da an ce hanawa ki ke yi, ni kuma na yi nasara na shigo, mu zuba da ni dake". "Lallai yaro bai san wuta ba sai ya taka, ga fili ga mai doki". Har hafsa ta kwana bakwai a gidan nan, ba su haɗa shimfiɗa da Alhaji mu'zzam ba, duk ɗokin amarcin da take yi, komai ya fita daga kanta, ta rasa abun da yake yi mata daɗi, ƙiri-ƙiri yake nuna mata shi ta matarsa yake yi ba ita ba, saɓanin abun da ya nuna mata a waje. Jauhar kuwa ta cigaba da yi wa master magiyar, ya taimaka ya bari ta je gidan hafsa tun da an yi bikin, kuma ta na son ta je gida ta gaida baba, ta bashi gudunmawar biki. "Ni fa nayi miki alƙawarin zuwa gidan yayrki, amma amarya ce, ya zaki je musu gida sati ɗaya da biki?" Cikin rashin fahimta ta ce "To ba a zuwa?" "Eh, idan sun shirya samun zuriya su, ai ba za so ki dame su ba, idan lokaci yayi zan kai ki". Anty da Rahila suka cigaba da yawon bin bokaye, ƙauye-ƙauye, dan su sake kama Alhaji mu'azzam, kuma ya saurari hafsa. Komai na buƙata gashi nan a zube, amma miji ya gagareta sai dai ta ganshi daga nesa. Tayi iya ƙoƙarinta, duk wanda ya zo, ba ta bari ya fuskanci tana cikin damuwa, ta baka abinci ka ci ka sha, idan zaka tafi ta baka na mota mai yawa, tayi ta hura hanci, saboda tana cikin gida na alfarma ga motoci a parking lot. Jauhar ta gaji da yi wa Al'amin magiya, ta ƙyale shi, dan kansa ya ce ta shirya, shi zai kaita gidan hafsan, su gaisa ya dawo da ita. Ta din ga murna tana yi masa godiya, amma ta ce "Dan Allah master a sakawa baburin nan salansar sa, idan muka fita fa saboda ƙarar da yake yi, sai kowa ya waiwayo ya kallemu". Ya ce "Ni fa na fi son abuna a haka" Ta kwantar da murya ta ce "Na sani, amma a taimaka mini, ko so kake kowa sai ya ɗaga kai ya kalli babyn robar taka?" "Zan duba" "Yauwwa master na" Yayi murmushi ya ce "Naki, waye ya baki?" Ta ce "Allah ne ya bani, kuma na karɓa hannu bibbiyu ina yi masa godiya" Ta kira hafsa a waya, hafsa ta ɗaga da ƙyar tana cika tana batsewa, Jauhar ta ce "Anty hafsa ina wuni, ina ta kiranki ba kya ɗagawa" "Bana kusa ne, shiyasa" "Adress ɗin gidan zaki bani, gobe in Allah ya kaimu zan zo in sha Allah" Kamar hafsa ta ce mata ba ta so, b tare da la'akari da su ba su taɓa taka gidan jauhar ba, amma sai ta ga ya dace jauhar ta zo ta ga daular da take ciki, dan haka ta bata adress ɗin. Bayan ta gama wayar, ta ce "Master ta bani adress ɗin, babu wuya ma gane gidan nata. Zo mu yi kallo a wayata" ta yi maganar tana zama a kusa da shi. "Ni kallon nan gajiyar da ni yake yi" Ta ce "Ahh haba dai, ko kaɗan nan, yana da kyau ka samu abubuwan da za su din ga ɗebe maka kewa" Al'amin ya ce "To zaɓi ɗaya, ko dai ki sauke wannan abun, ko kuma a haƙura da kallon" yayi maganar yana nuna boti, da yayi ɗare-ɗare a kan cinyar jauhar. Jauhar ta kwashe da dariya ta ce "Boti master ya ce ka tashi daga cinyar matarsa" kwanciya magen ya ƙara yi, yana lafewa. "Ban taɓa ganin abun da ya raina ni ba, kamar ke da magen nan ba" Jauhar ta din ga dariya, ita yadda ba sa ga maciji da botin ma dariya yake bata. Ta zauna a kusa da shi, tayi connecting da mp, ta saka musu film. Ta kalleshi ta ce "Ka ji ko? Baby ake cewa mace, kai baka yi mini irin wannan kalar soyayyar, sai zare mini ido da sakani kuka" Yayi murmushi bai ce mata komai ba, sai dai ta ji ya saka hannayensa ya riƙe nata. Mintuna goma da ta ɗaga kai ta ga yayi bacci. Ta zuba masa ido yana bacci, a ranta ta cigaba da yi masa addu'a. Ta kashe wayar ta ce "Master ka tashi ka je ka kwanta tun da kallon ne ba ka so" Yayi shiru bai motsa ba. "Master" "Mmm" ya amsa ba tare da ya buɗe idonsa ba. "Mu je na yi maka addu'a ka kwanta" Ya ce "Ɗauke ni, na gaji" Ta ce "Na ɗauke ka, ai kuwa da sai dai wata ba ni ba, aikin me ka yi ka gaji har haka?" "Ƙasa muka kwashe tifa biyar, ban sha komai ba kuma na yi aikin, ni da su Walid" Jikinta a sanyaye ta ce "Har tifa biyar master. Baka gaya mini ba sannu, amma dai sun biya ku ko?" Ya tashi zaune ya ce "Eh, har na kai wa mai solar kuɗin, ya zo ya saka miki solar, ya kawo miki fankar solar zafi ya fara yawa kuma ba wuta". "Solar kuma master? Da mun sai kayan abinci, zafi lokaci ne zai wuce, solar fa da tsada". "An ce masu asma, ba sa son zafi" ya yi maganar yana tashi tsaye, tashi ta yi ita ma, sai ta rasa me za ta ce masa, ya nufi ɗakinsa, ta rasa ta ina yakamata ta fara ma. Akwai abubuwa masu muhimmanci da yakamata ace yana yi da kuɗi, da solar da ya saya, kamata yayi ace ya sai musu kayan abinci, ya ɗinka sutura da ko ɗan takalmi ne mai kyau na kwalliya. Duk in da ya kwashi taklminsa soso haka yake ƙarawa gaba da su, kayansa ma ita ta ware masu kyan ta kai ɗakinta, sai idan za shi wani wuri na musamman ko juma'a ta bashi ya saka. Sai dai ta san bai kyautu, ta nuna ba ta ji daɗin abun da yayi ba, domin ko ba komai, yayi ne dan ya kyautata mata. Ya nemi wuri ya kwanta, ta zauna a kan katifar, ta ɗora hannunta a kansa, tare da karanto masa addu'oin kwanciya bacci. Abun da jauhar ba ta sani ba, bayan ciyar da shi da ta din ga yi farkon auren su, Addu'ar da ya ji tana yi masa cikin magagin ciwo, tayi matukar tasiri a zuciyarsa, Addu'a ce da idan ba uwa ba, ba kowa zai yi maka ba. Addu'oin da take yi masa idan yayi mata wani abu na kyautatawa ma, ba ƙaramin daɗi yake ji ba. Ga uwa uba kirarin da take yi masa wasu lokutan, da suke fasa masa kai. Duk wani abu da zai yi baya manta tarin alkhairin ta. "Allah ya saka maka da alkhairi, ya buɗa arzikin ka, ya wadata mu da halal ya nesanta mu da haramun. Na gode sosai da sosai Allah ya biya ka da gidan aljanna, ya jiƙan iyayenmu" Idonsa a lumshe ya ce "Amin 'yar aljanna, addu'ar ta yi daɗi" tayi murmushi ta tashi. Washegari da wuri ta shirya, tana ta murna za ta je gidan hafsa, ta wanke laifinta na rashin zuwa biki. Shi kuma ya ce zai kaita, amma ya din ga yanƙwanata. Ba su fita ba sai sha ɗaya saura, tiryan-tiryan, har gidan hafsa. Gida ne babba na gaske, Al'amin ya ce "Ba daɗewa zaki yi ba, da wuri zan dawo mu tafi" "To Allah ya dawo da kai lafiya, take care". Ya ce "To, ki shiga, sai na tafi" "Saboda kar in gudu?" "Idan kin gudu ma zaki dawo" yayi maganar yana tayar da babur ɗin sa. Juahar ta shiga har falon Hafsat, ta din ga bata haƙuri na rashin zuwanta bikin nan ta ce "Kin san halik maza wasu lokutan sai a hankali, babu yadda ban yi ba, amma ya hana, ba shi da lafiya lokacin" Hafsa sai ɗan fizgar kai take yi, wai ita dole ga matar mai kuɗi. Har la'asar tana gidan hafsa, bayan ta gama shan ƙamshin, ta saki jiki kuma suka hau hira, da yake ita ce sakuwar jauhar, daga ita sai jauhar. Ta din ga koɗa mata irin son da Alhaji mu'zzam yake yi mata, dan ta tura mata haushi. Jauhar kuwa ko a jikinta, ta ce "Wallahi yaya hafsa idan Allah ya baka miji mai sonka tsakani da Allah, duk wani ƙalubale mai sauƙi ne" Ta ce "Aikuwa shiyasa nake tausyinki, aure ba soyayya, ga miji sai a hankali" Jauhar ta ce "Aikuwa ke da ki ka yi na soyayyar ma, ba ki fi ni samun kulawa ba, da farko a tsorace nake da shi, tun da muka saba Alhamdilillah" "Taɓ, haryanzu yana safarar cocaine ɗin?" Duk da jauhar ta ji haushin maganar ta ce "Da safarar cocaine yake, ai mun girmi zaman Kano sai Abuja" Al'amin ya kira jauhar, ya ce ya zo ta fito su tafi. Ta leƙa ta window falo ta hango shi, a cikin harabar gidan. Ta ce "Ɗago kanka sama ka ga" ya ɗaga kai, ya hangota. "To ka tafi, ba yau zan dawo gida ba, sai gobe" "Wallahi idan ba ki fito ba, zan shigo har ciki" "Kaikaikai, gidan mutanen za ka shigo?" "Sai na shigo ɗin tukuna kenan?" Tayi dariya ta ce "A'a, rufa mini asiri, kar ka saka da ni da kai a zanemu, gani nan" Hafsa ta yi ƙuri da ido, tana kallon jauhar, tana leƙen Al'amin kuma suna waya, tana ta dariya. "Yaya hafsa, bari na tafi" Hafsa ta tashi ta ce "Mu je na raka ki". Suka fito harabar gidan tare, yanayin Al'amin a yanzu, akwai nutsuwa a tare da shi, ba kamar lokacin da ya je gidan su ya ɗauki jauhar ba. Hafsa ta ce masa "Ina wuni?" "Lafiya ƙalau" ya amsa idonsa a kan jauhar. "Ya ka ke hararata ne, ba gani na fito ba" Ya ce "Zaki yi bayani" motar Alhaji mu'azzam ce ta shigo gidan, yana hangen jauhar, ya ci wani irin wawan burki ya buɗe motar ya fito. Ya ƙaraso ya kalli Jauhar ya ce "Jauhar, dama kina nan?" Tayi murmushi ta ce masa "Eh, ina wuni?" "Lafiya ƙalau jauhar, sai dawowa na yi aka ce mini kin yi aure, na ce ko wani laifin na yi miki? Hafsa ta ce mini dama akwai wanda ki ke so, shi ki ka aura, ni kuma baki gaya mini ba lokacin da nake neman aurenki" Kallo ɗaya jauhar ta yi wa Al'amin, ta ga ya murtuke fuska, idonsa ya fara kaɗawa zuwa ja. Ta ce "Eh, gashi nan a gabanka mijin nawa, Allah dama ya ƙaddara yayata zaka aura. Yaya hafsa sai anjima". Ya ce "Tsaya na baki na mota" ya saka hannu a aljihunsa ya ɗebo kuɗin da bai san yawan su ba, ya miƙa mata ta girgiza kai ta ce "A'a na gode" Hafsa ta ce "Baby kawo ka ga" ta karɓi kuɗin ta turawa jauhar a jakarta, ta ce ba a mayar da kyautar manya, ku gaida gida. Tuni Al'amin ya juya ya fice, idan ya cigaba da tsayuwa, zai iya yi wa Alhaji mu'azzam illa, da wuƙar da take cikin rigarsa a soke. Tun da suka tafi hanya, bai ce mata uffan ba, hakan ya sanya ta cikin matsanancin tashin hankali. Da ya ajiyeta a gidan ma, tafiyar sa yayi, bai ko shiga gidan ba. Ta din ga addu'a Allah ya sanyaya masa zuciyarsa. Duk yadda ya so ya sarrafa kansa ya kasa, sai da yayi shaye-shaye, domin rage raɗaɗin abun da yake ji, dan zuciyarsa har wani tururi take yi. Har sha biyun dare, idonta biyu tana zaune, tana jiran dawowarsa, ya koma mata Al'amin ɗin sa, dan ko sallama bai yi ba ya shigo, ya wuceta ya tafi ɗakinsa. Cikin fargaba, tana addu'a, ta bi bayansa, warin wiwi duk ya cik wurin. "Sannu da zuwa, nan zan kawo maka abincin?" "Fita ki bani wuri, kafin na kakkaryaki na zubar. Idan ba kya son zama da ni, ba sai kin wulaƙanta ni, ta hanyar kai ni wurin tsohon saurayinki ba, shiyasa nake ta baki zaɓi tuntuni a kan zama da ni, ba dan na sarrafa zuciyata ba, sai na kashe mutumin nan har lahira yau, fita ki bani wuri, bana ƙaunar ganinki ma". Ta marairaice ta ce "Dan girman Allah ka yi haƙuri, wallahi da na san zamu ganshi da ba mu je ba, ni saboda 'yar uwata na je". "Saboda 'yar uwakki, ko kuma saboda ki ganshi?" "Ya za ayi na je ganin wani, alhalin ina ɗauke da igiyar aurenka a kaina" "Ki daina wani kwantar da murya, na riga na gane abun da ki ke nufi, da in da ki ka dosa, if you still loves him zan iya sakin ki, ki iya koma wurinsa, tun kafin na illata ki, ba zan juri wannan cin fuskar ba, nan gaba ban san me zaki aikata ba" Cikin tsananin ɓacin rai ta ce "Idan ka sake ni, hakan baya nufin rayuwata ta zo ƙarshe, jaririn da ya zo duniya ma Allah ya na iya karɓar rayuwar mahaifiyar sa, kuma ya raya mata shi. Ka yi mini duk hukuncin da ka ga shi ya dace ni" ta fice daga ɗakin, cikin tsananin ɓacin rai da damuwa. Ransa yayi matuƙar ɓaci, jin yadda ta gaya masa maganganu, gashi dama a cake yake, ya nemi wata ƙwaya ya haɗiya ya kwanta, dan kar ayi ɓatacciya. Da asuba ya farka, ya saba ta zo tayi ta fama ta tashe shi, amma yau taƙi zuwa. Yayi sallar asuba, gari yayi haske ya fito, amma ba ta fito ba, ya gaji da zama ya fita. Da azahar ma, abincinsa ta ajiye masa ta yi zamanta a ɗaki, idan yana falo tana ɗakinta, idan yana ɗaki sannan zata fito. Ya shareta shi ma, yana jiran ta zo ta bashi haƙuri kamar yadda ta saba, amma taƙi, sai ya ji gidan yayi masa duhu babu daɗi. Kusan kwanaki uku, ba wanda yake shiga harkar wani. Yau har ya cire kaya ya kwanta, ya tashi ya zauna yayi shiru yana tariyo maganganun da ya gaggaya mata, sai ya ji sun ɗan yi nauyi da yawa. Ya tashi ya tafi ɗakinta, kasancewar babu wuta, ya kunna fitilar wayarsa, ya shiga. Tana banɗaki tana wanka, ta jingina fitilarta a kan mudubi, tana haska mata cikin toilet ɗin. Ya ƙarasa gaban mudubin, ya ɗauki wayar ya kashe fitilar. "Waye a nan?" Tayi maganar cikin tsoro, dan ba ta san ma ya dawo ba. "Waye?" Yayi shiru bai yi magana ba. Da sauri ta gama kwara ruwan a jikinta, ta fito sai dai ɗakin yayi duhu, ba ta ganin komai. "Wai waye ne?" Tayi maganar tana laluba hanya. Direction ɗin da yake ta nufo, cikin tsoro, kawai ta ji ya zaunar da ita a kan cinyarsa. Cikin tsananin tsoro ta ware baki za ta yi ihu ya tsohe mata baki ya ce "Shhhhh, Al'min ne" Ayshercool 08081012143 39 🔞 LITTAFIN KUƊI NE ₦500 VIA 0009450228 AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143 YOUR RECEIPT VALIDATE YOUR PAYMENT. Cikin cunkusa baki ta ce "To kuma shi ne zaka tsorata ni? Ko gama wankan ban yi ba na fito" Ya ce "To mu je na ƙarasa miki" Tsuke bakinta ta yi ta kasa magana, jin abun da yake yi, da ba ta yi zato ba. Kasancewar bayanta, yana jikin ƙirjinsa, yana jin bugun zuciyarta yana fita da sauri-sauri. "Meyasa ki ke shareni? Kwana uku kin yi mini laifi, kuma kina gaba da ni ko?" Ba ta yi mamakin ƙarfin hali, da ƙwarewa a iya rainin hankali, irin na Al'amin ba, wato ma zaman jiran ta bashi haƙuri yake yi. "Kin san zaki yi gaba da ni, meyasa ki ka bari muka saba? Ba ni da saurin sabo, ki ka yaudare ni ki ka sa na fara sabawa da ke, shi ne zaki wani din ga mazewa. A din ga manta abu a kwana ɗaya ya wuce kawai a cigaba da life. Ni kaina ban san dalilin da ya sanya nake matuƙar jin baƙin ciki idan na ga wani abu ya raɓe ki ba" Da ƙarfi ta ce "Master" tayi maganar tana ƙoƙarin miƙewa. Hankali kwance ya ce "Yes" ba tare da daina abun da yake yi ba. Cikin rauni ta ce "Wai meye haka?" "Aure" ya bata amsa kai tsaye. Shiru yayi, jin yadda zuciyarta ke cigaba da bugawa da sauri, tana nema ta fara haki, saboda tsoro. A hankali ya ce "Common, relax mana" "Babyn roba" tayi masa shiru, "Kodayeke yanzu babyn ƙarfe ce, ki amsa mana" still ta yi masa shiru, yana jin yadda ta saka ƙarfinta ta riƙe hannunsa. Fito yake yi mata a kunne, hakan ya sanya ba shiri, ta saki hannunsa, ta toshe kunnenta. "Ki amsa mana, tambaya zan yi miki mai muhimmanci. Kin san bana mantuwa, kamar na'aura mai ƙwaƙwalwa nake, in dai ka ajiye zaka zo ka ɗauka. Idan ban manta ba kin ce kina so mu rayu tare. Ina ta tsoron taɓa abun da nake ganin ban dace da shi ba. Ba na son cutar da rayuwarki, in yi silar gurɓacewarta kamar yadda tawa ta gurɓata, duk da kin daɗe ki na nuna mini ina rintse ido, Al'amin ba ya abu bisa zalunci" "Na nuna maka me?" "In faɗa kenan, ko shekaranjiya meya kawo zancen zuriya? Ke 'yar yarinya kallonki kawai nake yi, amma kar ki damu da hakan ai lafiya ce" wato da wani ne yake ba wa jauhar labarin maganganun nan daga bakin Al'amin suke fitowa, sai ta ƙaryata, amma ƙiri-ƙiri, ya shige duhu yana sakin maganganu yadda yake so, alhalin ya ce ba ya jin komai. Tana cikin tunanin ta ji ya ce "Kin amince mu rayu tare, a matsayin abu guda? Ba na son cutar da ke, ke ma kin shiga ƙalubale da dama, bana son ki sake shiga matsalar rayuwa, rayuwarki ta tafi a haka kawai. Idan kin amince, zan yi iya ƙoƙarina wurin zama da ke da zuciya ɗaya, amma sai kin yi wa yanayin rayuwata uzuri, duk da a yanzu ma kin taka muhimmiyar rawa a rayuwata. Be mine" Haka kurum ta fara kuka, kukan da ba ta san na menene ba ma. "Talk babyn roba". "To ka ƙyale ni, gobe da asuba sai na gaya maka" Cikin buɗɗiyar muryarsa, da take fitowa daga ƙirjinsa, ya ce "Na ƙi wayon, yanzu zamu gama maganar" "Master" "Mmmm" "To zaka daina saka ni kuka?" Ya ce "In sha Allah" Ta ce "Zaka daina shaye-shaye?" "In sha Allah, ina iya ƙoƙarina, ba abu ne da zan daina lokaci ɗaya ba. Mu bar wannan maganar, baki bani amsa ta ba, zaki cigaba da zama da ni, a yadda nake, ina talaka marayan da ya rasa kulawa, sai bayan shigowar ki rayuwata?" Tana kuka ta ce "Dama ai kai ka ke cewa zaka sake ni, ka ke sakani kuka, ina son in zauna da kai" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Duk wani abu da ki ka yi mini na alkhairi, yana rubuce a ƙirjina, ba zai taɓa gogewa ba, ban taɓa mantawa da ko guda ɗaya ba, babu wata mace da ta taɓa playing role ɗin uwa a rayuwata sai babyn roba, bashi ne a kaina kulawar da ki ka yi mini". "Ni saboda Allah nake kula da kai" "Ni na isa in biya ki ne dama?" Jauhar ido yayi tsilli-tsilli, bayan da Al'amin ya ƙaryata tunaninta na ko ba shi da lafiya ne. Ya tabattar su a matsayin miji da mata. babu tsammani aka kawo wuta, haske ya gauraye ɗakin, Jauhar ta takure jikinta, sai rawa jikinta yake yi, yayi murmushi ya ja bargo ya rufeta. Ya zuba wa gashin kanta ido, ba baƙi ne wuluk ba, amma mai laushi irin na fulani, ya hargitse, ta cusa kanta cikin bargo sai gashin a waje. Ya daɗe yana kallonta, kafin ya kai hannunsa yana shafa gashin ya ce "Amm ya ma sunan angela ko?" Tayi masa shiru, ta sake dunƙulewa wuri ɗaya. Ya cire bargon daga fuskarta, amma ta rintse idanunta. "Kalleni mana, abu zan gaya miki fa" Ta cunkusa baki, tana ta jan majina a hancinta, fuskarta duk ta yi ja saboda kuka. Wani nishaɗi yake ji, ya cigaba da kallonta yana ta murmushi, kamar wanda aka yi wa Albishir da kujerar makka. Wayarsa da ta faɗa ƙasan gado ce, ta fara vibrating, ya juya ya zura hannunsa ya ɗaukota, ya sake matsawa kusa da jauhar, ya ɗaga wayar. "Maza" muryar liti tayi amsa kuwwa a wayar. "Mmm" "Kana ina ne?" A taƙaice ya ce "Gida" yayi maganar yana cigaba da shafa gashin jauhar. "Wai me ka ke yi ne? Ko baka da lafiya ne?" Al'amin ya ce "Meyafaru?" "To ai ji nayi kana amsawa kamar ana yi maka dole" "Ina jinka ya aka yi?" Liti ya ce "Akwai matsala ne fa" "Ta me?" "Yaran madaki, duk sun cire pastocin indabo, ka san ɗazu Walid da su guduma suka gama sasskawa, mu na dawowa muka tarar duk sun cire, ya tambaya aka ce masa yaran madaki ne, gashi can ya tafi, nayi-nayi ya ƙyale su, ya ɗau wuƙa ya tafi, shikaɗai kar su yi masa wani abun, ka san Walid da baƙin taurin kai, kamar jinjirin jaka, dan yafi jaki taurin kai" Al'amin ya ja guntun tsaki ya ce "Gani nan, bari na tafi cikin garin, maza ka kira yaran nan, ka yi magana da su guduma ma, zan kira yaran unguwar mu, maza su bishi kar su yi masa wani abun, gani nan" ya yinƙura zai tashi, jauhar ta ja jikinta ta riƙe shi ta ce "Rigima zaka je ka yi ko?" Ya girgiza mata kai ya ce "Ba rigima zan yi ba, amma idan har ba a kai masa ɗauki ba, za su iya kashe shi" Cikin takaici ta ce "Kana ganin halin da ka sakani, a  haka zaka tafi ka bar ni, a wannan yanayin da nake ciki?" Ya ɗagota ya ce "Ki yi haƙuri, bana son a sake asarar rai saboda ni, wallahi suka ga Walid shikaɗai, za su iya kashe shi, am sorry yanzu zan dawo, ki kwanta kar ki tashi kina buƙatar hutu" ya ƙarasa maganar yana kwantar da ita ya bar ɗakin. Ta lumshe idonta, hawaye suka cigaba da zuba, sai da ta yi ta gaji, sannan ta saukko daga kan gadon da kyar, ta haɗa ruwa mai ɗumi sosai ta tsarkake jikinta, ta nemi wuri ta kwanta. Da asuba da ƙyar ta tashi, ko alwala ba ta yi ba, ta tafi ɗakinsa ta duba, ko ya dawo cikin ƙoshin lafiya. Ƙarar buta ta jiyo a banɗakinsa, alamar yana alwala, wani ɗan sanyi ta ji a ranta, yau da kansa ya tashi sallar asuba, ko yaushe ya dawo ma oho. Ta koma ta yi salla, ta sake fitowa ta leƙa, ta ga yana salla, ga kayan shaye-shaye a kan katifarsa, ganin yana salla, ta shiga kanta tsaye, ta tattare kayan ta fice. Bacci ya ƙara kwasheta, tana cikin baccin ta ji ta a takure, ta yi miƙa ta buɗe idonta, ta saka a nasa. "Kalli agogo ƙarfe sha ɗaya, yunwa duk ta yi mini illa, na sayo ƙosai na kasa ci, ya ja mai, kuma farin maggi ya yi yawa a ciki sosai. 'ikon Allah, shi ko ɗan rarrashin nan ma ba zai yi bs, zancensa kawai abinci. A ƙule ta ce "In da ka tafi ba su baka abincin ba? "Me ki ka ce?" Ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Na ce in da ka tafi ba su baka abincin ba?". Ya ce "Ba su bani ba, ke zaki tashi ki bani yanzu" Kawai ta juya masa baya, dan daren jiya ta ƙulu yadda ya tafi ya bar ta. Ba ɗaga ƙafa, ba komai, ya ƙara huce baƙar maganar da ta gaya masa, ya gama ya tada kai da jikinta, ya lumshe ido ya hau bacci. Ta gama koke-kokenta, duk iya ƙoƙarin da tayi, ta ture shi ta tashi, ta kasa sai ma ji da tayi tana haki, Al'amin ya gama raina mata hankali ta ko ina. A haka har baccin dole ya sake yin gaba da ita. Ƙarshe har azahar ko wanke-wanke ba ta yi ba. Ta yi wanka, ta canza kaya, ta fito ya basar da ita, kamar babu abun da ya faru, ta tarar da shi da wayarta a hannunsa, yana game, ta share shi ta wuce, sai da ta fita ya bi bayanta da kallo yana murmushi. Ta tarar yayi wanke-wanke, ya share tsakar gidan tsaf, har markaɗen kayan miya ya kai. Ta dawo ta koma ɗakinta, ta ɗaukko bedsheet, zata fita ya ce "Me zaki yi ne?" "Wanki" "Me ya same shi, zaki wanke? Ko karyawa ba ki yi ba? Ki saka shi a baho, zan wanke, ki samu ki karya" Sai cika take tana batsewa, mazewa kawai yake yi, don dariya yake son yi, amma ya maze shi ma ya sha kunu. Tun da ya kai markaɗen nan, ya dawo bai sake fita ba, wuni guda yana gida, duk da babu wanda yake kula wani, amma zaman kula da ita yake yi. Har isha'i, kowa ya koma ɗakinsa, har ta kwanta, ta ji ya shigo ɗakin, kan tayi magana ya ƙaraso kan gadon ya hau. "Malam ya ne? Menene kuma?" "Kamar yaya?" Yayi maganar yana janyo bargonta, ya rufe ƙafarsa. Kamar tayi ihu ta ce "Menene kuma?" Ya ce "Da na kawo miki kajin mutum goma sha biyu, ki ka cinye ki ka yi kyautar wasu, kin tambayi ta mecece?" Cikin rashin fahimta ta ce "Ban gane ba, ka ce a gidan oganka ka karɓo". "To gaba sai ki dinga tambaya, kwaɗayayyiya, ki ka din ga ci kina rabarwa, ni sai dai ki sammini, yanzu kuma tambayata lafiya? Ba lafiya ba" Cikin rauni ta ce "Master" ya ce "Yes" "Dan Allah ka koma ɗakinka" ya kwanta ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan ɗaya ya ce "Zuriya fa ki ke so, ki ke wani basarwa" Jauhar ta yi danasanin faɗar maganar nan. Kawai ta zauna a zaune tana kallonsa, sai kaɗa ƙafa yake yi. "Zo ki kwanta, na ga lokacin da baki da lafiya, har wani ƙara lafewa ki ke yi, bisimillah" yayi maganar yana nuna mata ƙirjinsa. Pillow ta gyara ta kwanta a kai, ta ƙi kula shi, mutumin da suka wuni ba sa magana, saboda tsabar son tayar da tarzoma, ya lallaɓo yana tayar da wani tsohon zance. Da asuba ta riga shi tashi, ta shiga ta yi wanka, tayi alwala ta zo tana tashinsa, ƙarshe sai kusan shida da rabi suka yi sallar, bayan ya saka ta canza wani wankan da alwala. A wurin da tayi salla, ta kwanta a kan sallaya ta cigaba da bacci. Iya ƙoƙarin sa yake yi kar ya sha komai, ya kasa jurewa, kamar zai fita hayyacinsa, ya lallaɓa ya dawo ɗakinta, ya tarar tana kwance a ƙasa tana bacci, boti ma yayi lakur a kan sallayar yana bacci. Tankaɗe boti yayi can gaba, ya kwanta a kusa da ita, ya ƙura wa fuskarta ido, ya kai bakinsa ya sumbaci goshinta. A ranar aka saka wa jauhar fankar solar, da ƙwai, ta din ga murna tana yi masa godiya. Sai dai Al'amin ya uzzura mata, duk dare, sai ya ce mata wai shan fanka ya zo, zafi yake ji, sai da ta gaji ta ce "Dan Allah master ka ɗauke fankar nan taka ka mayar ɗakinka , ko na huta" Ya ce "A'a ai dama ke na sayawa, dan haka gara na din ga zuwa nan kawai ina shan isakar, idan na mayar da fankar can, bayan iska kuma takura mini za ta yi din ga yi". Ta ce "A taƙaice dai, ni ce fankar kenan?" Ya ce "Eh mana, ke ga taki fankar, ni kuma ga tawa" yayi maganar yana nuna ta. *** Kwanaki suka cigaba da tafiya, sai dai tsakanin Alhaji mu'azzam da Hafsa sai dai kallo, ranar da uwargidansa ta bari ya zo ɗakin hafsa, kawai ta ga ya nemi wuri ya kwanta. Duk da irin kunya da kawaici irin ta 'ya mace, sai da ta cire kunya ta ce "Wai ni Alhaji, menene matsayina a wurinka ne? Na kasa gane kan wannan al'amarin" Ya kalli hafsa ya ce "Jauhar, yakam... A fusace ta ce "Wace irin jauhar kuma? Wulaƙancin naka da rashin mutunci har ya fi da, ga mari ga tsinka jaka? Tun ranar da jauhar suka zo, ka rasa sukuni, ka ke kirana da sunanta ba na so" Ya ce "Am sorry mistake ne, ki ƙara haƙuri ki bani lokaci, na yi wa Safiyya Alƙawarin babu abun da zai shiga tsakanina da ke, har sai lokacin da ta samu nutsuwa hankalinta ya kwanta, tana cikin damuwa sosai da sosai, kin san tana da kishi ne sosai da sosai ". Kamar ta ɗura masa ashar ta ce "Au har gaya mata ka ke ba abun da ya shiga tsakanina da kai, har sai ta yadda? Ita take aurena kenan? Bakomai na gode, ta ci lokacinta when it comes to my turn, zata gane shayi ruwa ne" ya girgiza kai ya ce "Kin ga ba na son rigima, ba zaki zo ki sameni, ina zaune lafiya da iyalina ki ɗaga mini hankali ba Please, ina respecting farincikin matata sosai da sosai " Hafsa ta ja tsaki, ta fice ta bar masa ɗakin. Al'amin na zaune a falon Indabo, ana ta tattauna yadda al'amura za su tafi kafin lokacin zaɓe, dan wata ɗaya kawai ya rage babban zaɓe, wanda yake dai-dai da lokacin sallar layya. Ya rage daga Al'amin sai P.A da Indabo yana ta sake jaddadawa Al'amin, idan aka ci kujerar nan za su ji daɗi, dan tun yanzu an ce masa idan ya samu senator ɗin nan, akwai vacancyn mutum uku za a bashi a NNPC. Al'amin ya ce "A cikin yarana, ko Nura guduma ne, ina son a samo masa aiki ko direban manyan motoci ne, yana can na saka ana koya masa jan manyan motoci" Indabo ya ce "Ba ka da matsala, kawai ku yi aikinku, duk akwatin da ku ka ga zata bayar da matsala, ku tayar da tarzoma. Maganar da nake yi maka, a yarjejeniyar da muka yi da uwar jami'iyya ta ƙasa, kan na dawo cikinta, nan da wasu shekaru, za a tsayar da Abdul takarar mataimakin gwamna" Al'amin ya ce "Har masu shaye-shaye ake tsayarwa su yi jagorancin al'umma kenan?" "Shaye-shaye kuma, yaron da yake karatu a waje, in sha Allah shi zai zama mutum mai ƙarancin shekaru da zai zama gwamna" "Menene sadakin aikina?" Indabo ya ce "Me ka ke so ayi?" Hajiya Bilki ce matar indabo ta shigo da laces, da atamfofi da lesuna sun kai talatin a hannunta, ta shigo ta zube a gaban Indabo. Ya kalleta ya ce "Madam ya dai?" Ta ce "Kala goma zan zaɓa ka saya" "Ke dai kullum cikin ɗinka tsumma, ko gajiya ba kya yi" "Kana shirin zama distinguish, ba dole na ɗinka sutura ina shiga ina fita, ina barazana ba". Indabo ya ce "To ki ɗauka, ina ta jiran Kwamishinan ayyuka ne, rage kuɗin wata kwangila, mu ƙara rage na campaign, ya haɗa kayansa yana kan katanga, jami'iyyar da tayi nasara zai koma da an yi zaɓe. Ala'amin ya tashi ya tafi gaban kayan, ya zaɓo zuƙa-zuƙan lesuna, guda uku, da atamfa uku. Indabo ya ce "Yaya saya zaka yi?" "Kai dai zaka saya, daga cikin sadakin aikina". Hajiya Bilki ta ce "Kai, lesunna hannunk fa dubu tamanin guda biyu, ɗaya dubu hamsin da takwas, atamfofin nan dubu arba'in da biyar, har nawa zai baka? Kuɗin da yawa ai" Ya kalleta ya ce "Ke zaki biya? Kuɗin kwangilar mutane za a sata a biya miki ai, wannan ma ya biya, ai ba kyauta zai bani ba, jinina da rayuwata zan saka a hatsari dan samun nasararsa. Ya miƙe da kayan a hannunsa, ya kalli Indabo ya ce "Sauran kuɗina za su zama ajalan a kanka, komai daren daɗewa zan waiwaye su, yadda ku ke ƙwamusar kuɗin mutane ta gajimare dole a din ga kasawa da mu, idan ana son a ga dai-dai, tun da damu ake wahalar waccan 'yar yarinyar ta gidana, itama yakamata a din ga damawa da ita. Kuma rabon tallafin karatu ma, a saka mini ita a ciki" Indabo ya ce "Aminu kenan, shikenan jeka Allah ya taimaka" Ya haɗa hannayensa biyu ya ce "Sa'a dai" ya fice daga falon. Hajiya Bilki ta ce "Gaskiya honorable, yaron nan yana wuce gona da iri, kamar tsoronsa ka ke ji" Ya ce "Ba tsoronsa nake ji ba, aikin da yake yi mini yana da yawa, kasada duk girmanta yana ɗauka. Akwai lokacin da tilas na yakice shi ai". Al'amin bai shiga da kayan gida ba, sai cefane da yayi na abincin dare. Ya tarar ta yi dambu tayi wa dambun miyar jajjage, da salad da awara. "Ke dai Allah ya yi miki iyayi, dambun da ake sakawa mai, ki ke yi wa miya, har da wata munafukar awara". Jauhar ta ce "Idan munafuka ce, bamu mu raba da ni da boti, shikenan ba canji, kullum sai dai dambu da mai? Ai gara a din ga upgrading" "Sai dai ya mutu da yunwa kuwa, to ai awarar ce, 'yar kaɗan" "Wai master ba ka iya abun 'yan gayu ba? Babu naman da zan saka a cikin miyar, sai na haɗa da awara, bai bada ma'ana ba? Ko sai an cika kwanon da awarar passion ce a kai" Ya taɓr baki ya ce "Eh to, gashi nan dai, zoɓon ma kamar yayi tsami, amma kwantai ne na jiya ne ko?" "Mmmm, na waccan shekarar ne" ta bashi amsa tana cigaba da aikin gabanta, na shirya stone. Tsoknarta yake yi, ya matsata tayi tsiwa, ita kuma taƙi. "Yaushe WAEC ɗin ku za ta fito ne?" Jiki a sanyaye ta ce "Ta kusa, har ba na son tunawa da ita" "Saboda ba ki yi abun arziki ba ko?" "A'a lokacin kana tsare, bana iya karatun" Ya ɗan rausayar da kai ya ce "Eyya, abun tausayi, Yallaɓai dan Allah ku sake shi, ba shi da laifi, laifina ne, wallahi ba shi da lafiya ma, master dan Allah ka gaya musu ba ka da laifi" yayi maganar cikin sigar kwaikwayon yadda ta yi waccan ranar. Murmushi ta yi ta ce "Kada Allah ya kawo abun da ba zai wuce ba, a lokacin nan ji nake a duniya kamar nikaɗai aka tsana wallahi. Da aka ce mini an kai ka prison, kawai na saddaƙar ciwon zuciya ya kama ni, kuma wai ka ce kar a kaini na ganka, ai na ji haushi, a duniya ba zan manta da su yaya walid ba, duk da suna taimakawa wurin ƙara ingizaka a shaye-shaye, amma sun tsaya tare da ni a lokacin da kow yake ganin idan ya taimaka mini zai kwana a ciki" Ya ce "Allah sarki 'yar madara, ba na son in ga kina kukan nan ne, ko kina yi wa 'yan sanda magana, suna wani yanƙwana mini ke, raina ɓaci yake yi shiyasa na ce kar a sake kawo ki". Ta ce "Gashi ya wuce, duk da lokacin gani nake kamar ba zai wuce ɗin ba" Ta tashi ta shiga ɗaki, ta dawo ta tarar da robar alawar madarar da take sayarwa, a gefensa bakinsa kuma yana ta tauna, ta ɗaga robar ta ce "Alawata ka ke sha ko?" "Eh, ta guda uku na sha sittin, a rage mini naira goma hamsin kenan" Sororo take kallonsa, "To ai ba a jikina ake tatso madarar ba, da zan sayar da ita ashirin ashirin, naira hamsin ce fa duk ɗaya " Ya waro ido ya ce "Ki ji tsoron Allah, har na sha ta ɗari da hamsin, gaskiya saba'in zan bayar". Abun da yake so ya gani ɗin ta fara, shagwaɓa tana cewa sai ya biya ta. "Gaskiya bani da kuɗi yanzu, zo ki shanye abarki" ya fito mata da harshen sa. Ta harare shi ta ce "Bana so, kuma idan na zo yi maka wanki na tsinci kuɗi, sun zama nawa" "Eh ai dama kin saba kwashe mini 'yan canjina, da kayan cajina shiyasa ki ke yi mini wanki ba dan Allah ki ke yi ba" ya tashi kamar zai tafi, amma ya riƙeta, yayi kissing ɗin ta, ya ce "To kin ga tare muka shanye, yanzu talatin ma zan baki" ya saka hannu a aljihunsa ya ciro dubu biyu ya ɗora mata a wuyanta ya ce "Gashi nan, uwar son kuɗi" "Ai talatin ka ce zaka bani, saura dubu ɗaya, dubu uku yakamata ka bani" Ya ce "Biyoni ɗaki ki karɓa" Ta ce "A'a na yafe maka sauran, amma kar ka sake" Sosai wani bond mai ƙarfin gaske ya shiga tsakaninta da shi, har mamakinsa take yi, duk da mai hali baya fasawa, idan miskilancinsa ya motsa, ko kuma ya cake, ba ya sarrafuwa ta daɗi, amma haka take jurewa. Ga babban abun da yake ci mata tuwo a ƙwarya yanzu, wasu lokutan idan ya dawo daga shaye-shayen sa, da ƙaurinsa da komai yake zuwar mata, gashi ba abu ne mai sauƙi ba, ta nuna masa hakan ba, dole sai ta cikin hikima da dabara. Haka zata zauna, komai daren da zai yi sai ta jira dawowarsa, ta saka shi yayi wanka, ya canza kaya. Yau bayan ya bar ɗakinta, bayan ta idar da salla ta je ta same shi, a zaune a kan katifa. Ta ɗauki kwalin sigarin gabansa, ta ciro guda uku ta bashi ta ce "Wannan ta isa, kar a sha sama da haka dan Allah" "Bani in je ƙofar gida in sha" Ta ce "A'a ai shan nake so ka rage sosai da sosai, wannan ta isa" Ya juya mata baya ya shanye, tana zaune tana jiransa, ta bubbuɗe window, saboda hayaƙin ya fita. Jira yake ta fita ya kuma kunna wata, amma ta cire masa shirt ɗin jikinsa, ta ce ya kwanta, ya kwanta yana jiran ta fita, amma ta kwanta a jikinsa, a hankali ta din ga karanto azkar ɗin safiya. Babbar salla na ta ƙaratowa, jauhar hada-hadar neman kuɗi, ta cigaba da kankama, Al'amin bai taɓa saka ido a kan abun da take samu ba, dan yanzu iya ƙoƙarin sa yake yi, ya yi cefanensa, duk da kuɗin da take ɗan samu, in dai ya ji kuɗi a jikinsa, a kaso ɗari tamanin, ita zai kashewa, bai fi ya ƙarar da kaso ashirin ba, goma ya rabar goma ya yi shaye-shaye. Idan ta fuskanci da kuɗi a hannunsa, ta din ga lallaɓa shi kenan, ayi wani abu mai muhimmanci, idan ba haka ba, ba zai sai abubuwan da suka fi buƙata ba. Kuma babbar hanyar samun kuɗinsa, wurin Indabo, ya din ga tatsarsa kamar mai, duk da yana samun hanyoyin samun kuɗi yanzu, tun da kakar siyasa ce. Ana jibi salla, ya ba wa jauhar kuɗi, wai tayi kitson salla ita ma, ta je ayi mata zane a hannunta. Ta dawo ta tarar da kaya a kan gadonta, ta zazzage taga kaya na alfarma duk an ɗinka su, har da takalmi da turare. Mamaki ya cikata, yana dawowa ta fito falo ta ce "Master kayan waye a kan gadona?" "Na kishiyarki ne" "Wace kishiyata?" "Ban sani ba, ko ina da wata matar ne bayan ke" Gaba ɗaya ta rikice ta ce "Master wai nawa ne Gaba ɗaya?" Ya ce "Naki ne babyn roba" Har ƙasa jauhar ta durƙusa tana yi masa godiya, ta rasa ma wace kalar godiya za ta yi masa, har da matse ƙwalla. "Ni ba irin wannan godiyar nake so ba, a sheƙa mini girki, a yi wa fankata caji, in sha iska sosai" sunkuyar da kai ta yi, cikin matsananciyar jin kunya. "Allah ya ƙarawa fankata gudu, tana ba da iska sassanya, ƙarfin gudunta, bai sanya tana bada iska mai cutarwa ba" "Amm bari na je na yi jajjage" ta juya ta nufi ɗaki. "Dama a ɗaki a jajjagen" ko waiwayowa ba ta yi ba, ta shige. Ranar idin babbar salla ma, tare suka tafi sallar idi. Ta sha kwalliya, tayi kyau sosai da sosai, a abun da bai fi wata guda ba, ta yi ƙiba fatarta ta ƙara fresh. Ta sha ɗaurin ɗan kwali, hannunta yayi kyau da zanen lalle ja da baƙi. Su liti suka din ga kiransa a waya, suna jiransa, yaƙi fita, sai da suka zo har gida sannan suka fita da shi, bayan sun kwashi wainar masa da sinasir da miyar agushi. Bayan la'asar sosai, ya dawo gida da nama kaya guda, har da karfatar sa, ga kayan ciki da uban nama. Kamar tayi kuka ta ce "Master, aiki daf da magariba ya zan yi?" "Ke da aiki ba ya yi miki wahala, ɗan wannan aikin zaki yi raki?". "To aikuwa sai ka tayani, kuma ba ka sayo itace ba" Ya kalleta ya ce "Ba a yi a gas, an hanaki shiga hayaƙi". "Gas ɗin dubu nawa za a zuba? Dole sai a itace" Ya kalli naman, ya ce "Ki shiga ciki, bari na aika nura ya sayo itacen, su walid suna waje, sai su shigo mu yayyanka" Ƙarshe dai hayaƙin da ba ya so, sai da ta shiga, har sha biyun dare suna aiki ita da shi. Duk da haka aikin bai ƙare ba, sai washegari, ta ce masa tana son zuwa gida, ya ce sai ta gama yi masa kwalliyar salla kan ta fita. Ya samu dambun nama da cin-cin, ya din ga tumurmusa, jauhar ta ce "Ni ban gane wannan lamarin ba, gaskiya rabawa za ayi. Kana ta ci idan cikinka ya ɓaci babu ruwana". "Ke ki ke da ruwa kuwa". Sai huɗu ga salla, sannan ya bari ta je gida, ya kaita da kansa. Aka yi sa'a Hafsa ma ta je gidan, tun da ta jauhar ta je, suke kallonta da kayan jikinta. Sai da mama ta magantu ta ce "Jauhar wannan leshin fa?" "Mama kayan salla ne" "Kin san kuɗin leshin nan kuwa?" Ta girgiza kai ta ce "A'a shi ne ya kawo mini" Ta kalleta ta ce "Wai sana'ar me yake yi haka ne?" Tayi murmushi ta ce "Yana sana'oin sa, kuma kin san yana tare da 'yan siyasa". Hafsa ta din ga kallon jauhar, yadda take komai nata cikin walwala, kamar ba ta da wata damuwa, duk da tana auren ɗan daba. Bayan jauhar ta ba su nama, dambun nma da cincin, aka din ga gaya wa jauhar, ai mijin hafsa rago ya kawo. Ta ce "Masha Allah, Allah ya saka da alkhairi" Duk yadda Hafsa ta so mazewa, sai da yanayin ta ya nuna akwai damuwa. Sai yamma Al'amin ya dawo, ya ce ta fito su tafi, babu yadda ba ta yi da shi ba, amma ya ce ba zai shiga ba. Gidansu ma da ya kaita, a waje ya tsaya, a gurguje jauhar ta shiga ta gaisa da Rahila, ta bata naman sallar sai dai ita ma, kayan jauhar kawai take kallo. Ana gama bikin salla, aka shiga hada-hadar zaɓe. Hankalin jauhar ya kasa kwanciya, saboda yawan shige da ficen da yake yi yawa. Yau ake zaɓen sanatoci, dan haka tun kan ta tashi daga bacci ya fice. Har yamma shiru bai dawo ba, kuma wayarsa ba ta shiga. Gaba ɗaya jikinta a sanyaye yake, jikinta  ya din ga bata akwai matsala, har bayan magariba bai dawo ba. Jin ana knocking ɗin gate, gabanta ya faɗi, ta saka hijjabi ta fito, ta ga Nura guduma a tsaye ta ce "Yaya wannan karon me kuma yayi?" Ya ce "Ki sako hijjabinki mu tafi" "Mu tafi ina?" "Asibiti!" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un!" Ayshercool 08081012143. 40 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Muryarta na rawa ta ce "Meyafaru? Wani abun ne ya same shi, ko ya yi wa wani?" Ya ce "Ni ma ban sani ba, oga walid ne ya ce "In zo mu tafi tare " Jikinta a sanyaye, ta kulle gidan, ta bi Nura guduma suka tafi, suna tafe tana ta addu'a a ranta. Wani private clinic suka je, emergency suka nufa, ana ta kai komo da matasa, da aka ji wa raunuka daga wurare daban-daban na harkar zaɓe, kasancewar an yi tarzoma sosai da sosai a wasu wuraren, kuma nan asibitin ne mafi kusa. Da ƙyar take iya ɗaga ƙafarta, wani irin yammmm haka jikinta yake yi mata, saboda tsoro da tashin hankali. A ƙofar wani ɗaki, ta tarar da Walid hankalinsa a tashe, yana kaiwa yana komowa. "Yaya walid, meyasame shi? Ko mutuwa yayi?" Walid ya ce "Ki nutsu ba mutuwa yayi ba, yana ta kiran sunanki ne kafin mu zo nan". "To meya same shi, yana ina?" Ganin likita ya fito daga ɗakin da yake facing ɗin su, ya sanya ta saka kai ta shiga ita ma. Gigicewa ta yi, ganin Wuƙa a kwiɓin Al'amin a tsaye tsororo, jini baya zuba, amma tana jikinsa, ga gefen kansa, an naɗe shi da bandeji. An saka masa oxygen, gefe ga oxymetre na reading vitals ɗin sa. Cikin kuka ta ce" Innalillahi wa Innalillahi raji'un, meya same shi haka? Waye yayi masa haka, Master dan Allah ka tashi, kar ku ce mini mutuwa yayi" tayi maganar tana rirriƙe hannunsa cikin tsananin tashin hankali. Kukan jauhar ya janyo hankalin likitoci, da m'aikatan jinya, suka ce meyasa aka bari ta shiga? Da ƙyar aka fito da jauhar ana rarrashinta, aka tabattar mata da yana da rai, tiyata za a shiga da shi a cire masa wuƙar, sai a duba  kansa. Cikin tashin hankali ta ce "Dan Allah likita zai rayu?" "In sha Allah, da kun biya kuɗin za a shiga da shi" Ta kalli Walid ta ce "Yaya Walid, nawa ne kuɗin?" Walid ya ce "Kuɗin da yawa, P.A ɗin Indabo muke kira, su biya kuɗin, hannunmu kuɗin ba za su kai ba ayi masa aikin" "Ka gani ko? Sun ma ƙi ɗaga wayar, su suna can hankalinsu a kwance, suna jiran sakamakon zaɓe, ni kuma an kassara shi, wannan tashinsa ai sai Allah" Liti ya ce "Ki yi haƙuri, in sha Allah zai tashi" "Nawa ne kuɗin?" "Da ɗan yawa, ki bari kawai" Ta girgiza kai ta ce "Ni ku gaya mini dan Allah, a nema tun da wuri, wuƙa ce fa a cikinsa" tayi maganar tana wata irin ajiyar zuciya mai ban tsoro. Suka din ga rarrashinta, amma taƙi saurarsu, Liti ya ce "Bari na yi gaggawa na je na samu wannan banzan mutumin P.A, ko dai a san yadda za ayi a biya, wallahi ko mu jiƙa musu aiki" Jauhar kamar za ta yi hauka, ƙarfin Addu'a ne kawai ya saka mata nutsuwa, ta din ga kaiwa tana komowa, gashi an ce ba zata sake shiga ta ganshi ba. Jauhar ba ta san yadda aka yi ba, liti da Nura guduma suka dawo da kuɗi, suka biya. Ake ce ana buƙatar jini, dan da yiwuwar ana cire wuƙar, jini ya ɓalle. Haka suka din ga zirga-zirga, jauhar itakaɗai a cikin su, babu wani daga danginsa, babu daga nata. Nura guduma ne ya bayar da jininsa, dan shi ne yayi dai-dai da na Al'amin, aka shiga da shi tiyata. Hawaye suka kasa barin idanunta, zuciyarta ta din ga wani irin zafi, ba ta taɓa tsanar wani abu ba, tsana mai muni sai yau duk da ba ta taɓa ganin indabo ba, tsananin haushinsa take ji, dan shi ne musababbin wannan tashin hankalin. Ta kai ta kawo, ta tsuguna tayi kuka, aka shafe sama da awa guda, ba a fito da shi ba, tayi alwala ta shimfiɗa ɗan kwalinta, ta tayar da salla, sai dai tana cikin sallar sai ta hau wasi-wasi, da tunanin me zai faru ta kasa nutsuwa. Babu tsammani likitocin suka fara fitowa, dan team ɗin tiyatar sun kai su biyar, gaba ɗaya suka nufe su, suna tambayar yaya?. Jagoran tiyatar ya ce "Alhamdilillah, an cire wuƙar, kamar yadda muka yi tsammani ya zubar da jini sosai, amma an saka masa jini, zamu kai shi ɗakin hutu, amma ba ma son a din ga shiga ana fita da sunan dubiya, kafin a kai shi ɗakin hutun, za a yi masa hoton kai, duk da saran da aka yi masa a ka bai yi zurfi ba, amma akwai buƙatar a duba". "Alhamdilillah ala kulli halin, Doctor mun gode Allah ya saka muku da alkhairi, ya jiƙan magabatanku, Allah ya sa ku gama da duniya lafiya ku bar aiki lafiya, ka da Allah ya wulakanta rayuwarku bayan ajiye aiki". Cikin farinciki suka din ga amsar addu'a jauhar, da Amin, tare da ba ta ƙwarin gwiwa a kan zai tashi ya warware gaba ɗaya. Bayan an yo hoton, suka tabattar da babu internal injury, jauhar ta zauna ta zuba masa ido, ga jini yana shiga jikinsa a hankali. Walid ya ce "Ina ganin ki koma gida, ko ni sai na kwana da shi a nan, kin ga idan ya tashi ba abun da zaki iya yi masa" "A'a idan na koma ba zan iya zama bama, hankalina ba zai kwanta ba, ni kawai ku bar ni". "To ai dole sai da namiji, ko zaki iya ɗaga shi, idan yana buƙatar hakan?" Cikin ƙwarin gwiwa ta jinjina kai alamar eh. Duk da alhini da suke ciki, sai da suka yi murmushi. Walid ya ce "Bakomai, ki kwana da shi, sai na kwanta a waje ni, idan ana buƙatar wani abun sai ki kira ni, yanzu bari na sayo wani abun, ki ci". "Bana jin yunwa" Haka suka kwana da Al'amin, amma bai farfaɗo ba. Ta din ga kallon wayarta, tana tunanin wa za ta kira, kamata yayi ace tana da wanda za ta kira, a kawo mata abun da zata buƙata saboda zaman asibiti, amma ta san ko za ayi mata sai an yanƙwanata ko gaya mata maganar da zata ɓata mata rai. Kwana suka yi likitoci na kaiwa da komowa a kansa, ƙarfe shida ta kira Abbu a waya, ya dawo daga masallaci kenan, ya ga kiran jauhar. Ya ɗaga a nitse suka gaisa. Ta gaya masa abun da ya faru, dumm ƙirjinsa ya buga, duk da ba wannan ne karon farko da Al'amin yake kai kansa in da ake cutar da shi ba. Abbu ya ce "Shikenan, ki yi haƙuri ki daina kuka, in sha Allah zan zo asibitin, daina kukan haka yarinyar kirki". Rahila da bacci take yi, sama-sama take jin sa ta ce "Lafiya, kai da waye?" "Matar Al'amin ce, wai suna asibiti an caka masa wuƙa a ciki jiya a wurin zaɓe" "Kai amma ka tsorata ni, shi ne ka ke ta rafka wannan salatin haka? Yau ya fara zuwa ayi masa illa a yawonsa? Dan Allah ka kwantar da hankalinka" Ya kalleta ya ce "Wuƙa a cikin sa fa aka ce mini, waya sani ma ko mutuwa yayi, Rahila Al'amin fa ɗa na ne, ba shi nake ƙi ba miyagun ɗabi'unsa ne ba na so" "Lallai kam na ga Alama, Allah ya bar soyayya" ta juya ta cigaba da bacci. Ƙarfe shidan, Nura guduma ya zo Asibitin, Walid ya saka ya raka jauhar gida, ta ɗebo kaya. Suka tafi, jikinta duk a sanyaye. "Dan Allah Nura kana ganin zai tashi?" Ya ce "Eh mana, in sha Allah, shi fa master ɗan baiwa ne, bar ganin abun da yake yi, yana da sa'a sosai da sosai in sha Allah zai tashi " "Amma ya aka yi aka yi masa haka?" "Wallahi ban sani ba, wai dai husuma ce ta tashi a wurin tattar sakamakon ƙananan hukumomi, amma ban san shi ya aka yi hakan ta faru ba" Jauhar ta ce "Allah ya sa ya tashi ya warke" Ya amsa mata da "Amin" Ko da taje gida, ta ɗebo kaya suka koma, Alluran da aka yi masa sun fara sakinsa, ya na 'yan maganganu a hankali. Ban da 'yar madara babu abun da yake kira, ta je ta zauna a kusa da shi, ta riƙe hannunsa, ta kifa kai tana kuka mai ban tausayi. "Gaskiya ƙanwa idan baki daina kukan nan ba sai kin tafi gida, duk muna jin abun da ki ke ji, daurewa muke yi, ba gashi yana magana ba ya kusa dawowa duka" Ta girgiza kai "Yaya walid ba ka san me nake ji bane" "Mun sani, amma ki yi haƙuri" Abbu ne yayi sallama, wanda jauhar ba ta taɓa tsammani ba, ta dai gaya masa ne kawai, kar ace ba ta faɗa ba. Da sauri ta tashi ta durƙusa ƙasa tana gaishe shi ya ce "Jauhar sannu ya mai jikin?" "Jiki da sauƙi Alhamdilillah" Su Walid ma duk suka gaishe shi. Ya ƙarasa gaban gadon, ya ƙura masa ido, ya ce "Ya aka yi abun ya faru" Tayi sauri ta ce "Zai dawo gida ne wasu suka yi masa haka da daddare" Kallon da su liti suka yi mata, ya sanya Abbu gane ƙarya take yi. "Yanzu ya ake ciki to?" Walid ya ce "An yi aiki an cire wuƙar" Ya jinjina kai ya ce "Alhamdilillah, Allah ya tashi kafaɗunsa" Suka amsa da "Amin" 'yar madara da yake ta maimaitawa ya sanya Abbu cewa "Wace 'yar madara kuma?". Gaba ɗaya suka kalli Jauhar, ta sunkuyar da kai cikin jin kunya. Abbu ya yi murmushi ya ce "Ikon Allah" Nurse ta shigo, ta ba su takarda a sayo magani. Abbu ya bayar da kuɗi aka sayo, ya din ga yi wa jauhar nasiha a kan ta nutsu ta kwantar da hankalinta, dan har a lokacin tana kuka. Sai dai wata nustuwa ta saukar masa, ganin Al'amin yayu ƙalau da shi. Har azahar suna tare da Abbu, daga bisani, ya ajiyewa jauhar kuɗi, ya ce "Duk yadda ake ciki su kira shi. Liti ne ya fita waje, ya kira P.A da wayar Al'amin, aikuwa ya ɗaga. Wata muguwar ashar ya narka wa P.A sannan ya ce "Saboda kai ɗan haramun ne, nake kiran wayarka tun jiya, ka ƙi ɗagawa. Saboda baku da mutunci daga kai har ubangidan naka, saboda kare ƙuri'arku, da ƙoƙarin hana ƙona sakateriya, yara sun fi sha biyar suka rufar masa da sara, ban da Mu ma akwai yaranmu a wurin da sai sun kashe shi, ka san ba maganin tauri yake sha ba, bakomai ba. Ka tsaya ka saurareni ma jiyan ka ƙi, da ƙyar aka samo kuɗin yi masa aiki, to wallahi ku saurari abun da zamu yi mu ma, wallahi hukumar zaɓen zamu cinnawa wuta, uban kowa ma ya rasa. Zaka gane ba ka da wayo daga kai har shi" "Ka ga tsaya, duk na san a cikin yaransa ne, ku yi haƙuri kun san yanayin halin da muke ciki ba a nutse muke.... "Halin da ku ke ciki ya fi rayuwarsa kenan? Ku sauraremu nan da wani lokaci" ya kashe wayar. Ya koma ɗakin da Al'amin yake, ya tarar da ya farfaɗo, har an ɗaga shi zaune ma, jauhar ta haɗa tea tana bashi, sai dai idanunta sun gaza daina zubar da hawaye. Al'amin ya zuba mata ido ya ce "Abbu ya zo nan?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "Dan ke ya zo ko bani ba? Ke ki ka yi masa magiyar ya zo?" "A'a" Walid ya ce "Liti mu ba su wuri, abun na baru ne" "Master" Ya kalleta, idanunsa sun yi ja, alamar yana jin jiki. "Ba na ce ka daina yi wa kanka illa ba, ko dan saboda ni? Sai zuciyata ta fashe hankalinka zai kwanta ko? In sha Allah kujerar nan ko ya sameta sai ta zame masa masifa. Ban taɓa yi wa wani muguwar addu'a ba amma na yi masa. Nayi nayi ka rabu da mutumin nan, ba mutumin arziki bane ba, amma ka ƙi aishikenan gashi nan yanzu ka janyo mana wahala". Ya lumshe idanunsa, dan ba ya son ya ga tana zubar da hawaye. Jauhar ba irin addu'a da ba ta ja wa indabo ba, dan shi ne kanwa uwar gamin ƙara ta'azzara rashin jin Al'amin. A washegari hukumar zaɓe, ta sanar da soke zaɓen ƙaramar hukuma uku, ciki har da ta su Al'amin wadda kuma take ta indabo, sakamakon tashe-tashen hankali da aka samu, da kuma ƙona wasu daga takardun da aka kaɗa ƙuri'a. Tuni P.A ya sanar da Indabo saƙon su Walid, kuma kansile ƙanan hukumomin, babbar barazana ce ga nasarar  indabon. Babu shiri, washegari da daddare suka shirya suka tafi wurin malamin su, da shi da P.A, malamin ya tabbatar musu da cewa, an samu tangarɗa a aikin da aka yi ne, yarinyar da yayi amfani da ita, ta haura shekarun da ake buƙatar, kuma a yanzu ba abun da zai iya yi musu, sai dai a bi wasu sabbin dabarun, a samu a haye. Suna tafe a hanya P.A ya ce "Honorable, wallahi yakamata ka duba mai zamani, da ƙyar idan ba yaransa ne, suka tayar da tarzoma ba, ka san dole zamu sake buƙatar su, mussaman yanzu da zaɓen ya zama inconclusive". Indabo ya ce "Matsalar yaron nan na ta ƙarewa wallahi" "To ya zamu yi, haƙuri zamu yi tun da muna amfanarsa". Indabo ya amince da hakan, P.A ya kira liti ya tambaye shi in da suke kwance Al'amin so yake Jauhar ta zauna a kusa da shi, ya ji ɗuminta su yi hira, amma alamu suka tabattar masa da fushi take yi, dan da tayi masa abun da za ta yi masa sai ta koma gefe, ta ɗauki wayarta tana karanta Alqur'ani. Ga kawo-kawo ɗin da ake yi, kuɗin hannunta duk sun ƙare, dan ma su liti suna tsaye suna tallafawa, kuma idan Abbu ya zo ya kan ba ta kuɗi, duk da zuwan nasa biyu ne kawai. Wajen ƙarfe ɗaya na dare ne, Ranar Walid da liti duk suna nan, duk da da facemask, a fuskar Indabo sai da suka gane shi, suka tashi suka ni bayansu. Jauhar ta ɗaga kai ta kallesu, Al'amin ya buɗe idonsa da yake a rufe a da. Jami'an tsaron suka bashi kujera ya zauna, yana kallon Al'amin da satar kallon jauhar. Ta tashi ta ce "Lafiya?" P.A ya ce "Baki gane ni bane, wanda ku ka zo wurina lokacin yana prison, honorable ne wannan, ya zo da kansa ba saƙo duba shi" ta haɗe rai sosai, kamar ya make shi ta huta haka take ji. Ya sauke facemask ya ce "Sannu kin ji, ya mai jikin?" Shiru tayi tana cigaba da haɗe rai. Ya kalli Al'amin ya ce "Wannan ce 'yar madarar kenan?" Al'amin ya ƙura masa ido, bai yi magana ba. Ya kalli Walid ya ce "Ba ya iya magana ne?" "Yana yi" "Dama cewa na yi bari na zo na ga yanayin jikin naka, Allah ya ƙara sauƙi. Ban sani ba ko ka samu labarin an soke mana wasu ƙuri'un abun bai yi daɗi ba, muna nan dai muna ta addu'a " Ya karkace ya ciro kuɗi kaya guda, ya miƙawa jauhar ya ce "Ga wannan a sai magani" Ta girgiza kai cikin takaici ta ce "Ba ma so, ka riƙe kuɗinka ni babban burina da fatana, ka fita daga rayuwar mijina, nima ina burin na ga ya shiryu ya zama mutumin kirki, kai ne ka ke saka shi aikata duk wani abu na rashin kyautawa. Idan ya shiga matsala kuma ka zame ka bar shi. Yanzu an riga an cuce ni, an tsugunar da shi. 'ya'yanka su suka fi cancanta su yi maka irin aikin da yake yi maka, tun da sun fi morarka, idan abun na Allah ne ka karɓi takardunsa ka sama masa abun yi mana, amma babban burnku yaran wasu su sha su bugu su sayar da rayuwarsu a banza gare ku". Ɗaya daga cikin jami'an tsaron ya daka mata tsawa, ta ce "Wallahi ko zaku kashe ni sai na faɗi gaskiya, nima 'ya ce, kuma na cancanci zama da nagartaccen miji, na san akwai iyaye da yawa da suke da burin ganin yaransu a hanya madaidaiciya amma duk hana hakan, ni dai dan Allah ka rabu da mijina, ka ƙyalemu" Maimakon ya ji haushi, sai yayi murmushin ya ce "P.A wato duk isa da kwarjinin namiji ya je gaban mace, sai abun da Allah ya yi, kalli Mai zamani a gaban matarsa. Aishikenan yarinya haryanzu baki san rayuwa ba, wannan yanayin mafita kawai ake nema, ki daina yi wa manya rashin kunya. Kuma mijinki zaki gaya wa ya daina abun da yake yi ba ni ba. Tun da a haka na ganshi, ki karɓi kuɗin nan". "Ba ma so, ba zamu karɓa ba" tayi maganar tana kuka. Ya miƙawa P.A kuɗin, ya karɓa ya miƙawa Viper, shi kuma ya karɓa. Indabo yayi murmushi ya fice da tawagarsa. "Master ni ka dizga ka kunyata a gaban mutane, gara ka cigaba da karɓar kuɗinsu kana shaye-shaye ana yi maka lahani, ni ko? Kai am tired na gaji, ba zan iya ba na sare. Na ɗauka abun mai sauƙi ne, amma ya wuce yadda nake tunani, you are not willing to change. Kana samun sauƙi gida zan koma, na gaji da auren" Liti ya ce "Subhanallah, dan Allah kar ki yi mana haka anty ƴar madara, muna murna Allah ya saya mana shi, kuma ki tafi ki barmu, ba fa shikaɗai ba har mu zamanki tare da shi muna amfana" "Eh, kuma har da ku ai, kullum ku kuke ƙara haɗuwa da shi, ku ke ƙara abun da bai kamata ba, Allah ya sa na mutu na huta". Duk wannan abun, yayi burus yaƙi magana. "In sha Allah, ba zaki mutu ba, ana mugun tare ai" "Ba wani tare, ku daina shaye-shaye mana, kuma kullum a kansa tsautsayi yake faɗawa, ni na gaji, yana warkewa tafiya zan yi na haƙura da zaman da shi" tayi maganar tana kuka, har ta fara tari mai haɗe da haki. "Mai laya" "Allah ya ƙara maka lafiya" "Ayi walƙiya, sai da safe" Walid ya ce "Iya wuya, yadda ka ke so haka za ayi" suka tashi suka fice, ya juya ya saukko daga kan gadon. Kamar ba ciwo ne a cikin sa ba, ya tunkaro in da take ya zauna, ya ƙura mata ido tayi shiru ta sunkuyar da kai, tana haki sama-sama. "Ki ka ce tafiya zaki yi?" "Eh" ta bashi amsa kai tsaye. "Yaushe?" "Kana warkewa gida zan koma, tun da ba ka so na, kullum cikin sakani ka ke a tashin hankali, na ce maka ba na son ka din ga zuwa in da za a ji maka ciwo, amma ka ƙi, ka dizgani a gaban wannan mutumin. Wallahi ba zan taɓa yafe masa ba, duk shi yake ƙara ɓata ka". "Yanzu abun da ki ka yi dai-dai ne? Ubangidana ne fa, ki ka tsaya kina yi masa rashin kunya". A ƙule ta ce "Shi dai-dai ɗin yayi mini, ba dan Allah ya yi da sauran kwananka a gaba ba, da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, ni na rasa in da zan saka raina, abun da nake ta tunanin zan iya ashe ya fi ƙarfina, shikenan". Gyara zamansa yayi, ya janyota jikinsa, yana kissing ɗin ta a hankali. She's not in mood, ta so ta ƙwace, sai dai kuma raunin jikinsa ya hanata yin hakan, kar ta fama masa. A hankali ya cire bakinsa daga nata yana kallon ta, amma ta haɗe rai tayi kicin-kicin. "Ki gaya wa likitocin nan su sallameni gobe, ko kuma na yi tafiyata" Da sauri ta kalleshi ta ce "A hakan ba ka warke ba?" "Eh na gaji da yadda ake zuwa ana magana da ke, haushi nake ji, shi kansa indabo shirun da nayi masa, shi ne mafi alkhairi da mummunan naushi zan yi masa" "Dan Allah ni ka daina taɓa ni, asibiti ne fa, idan wani ya shigo fa?" "To je ki rufe ƙofa ki dawo, zafi nake ji, ina buƙatar fankata, lamba uku kawai, ba sai an ƙure mata gudu ba" "Ko mafici ba zaka samu ba, ni rabu da ni" tayi maganar tana sake ture shi. Ya ƙi tashi ya din ga takura mata, duk dan ta sake ta ɗan samu nutsuwa daga fushin da take yi. "P.A wane mahaukaciya ne ya aura wa yarinyar nan mai zamani?" "Allah masani honorable" "Ikon Allah, kalarta kalar muryarta, ai rannan na kira ta ɗaga, kai ka ga yarinya zuƙeƙiya kamar ita tayi kanta. Amma kamar ta dace da aikin da malamin nan fa ya bayar, ya aka yi ba ka yi mini zancenta ba, gashi wannan an samu matsala" P.A ya ce "Honorable, kai ka san ba kowane kaya ne yake taɓuwa ba, idan aka taɓa wannan za a iya samun matsala, kuma na manta da ita ne gaba ɗaya wallahi" Indabo ya ce "Wace irin matsala? Ai tsaf za ta taɓu, ba tare da ya sani ba, idan ma ya sani na san yadda zan yi da shi. Lallai 'yar madara tayi kalar madarar sosai. Wannan yarinyar ita ce rauninsa kenan?" "Sosai kam, dan alamu sun nuna yana mugun sonta" Indabo yayi wani irin murmushi yana shafa tumbinsa. Maƙwabtan su Jauhar sun yi mata kara, na zuwa duba Al'amin, suka kakkai mata abinci, daga gidan su Baba ya je Saifu sai mama, sun je sun duba shi, duk da maman ta gaggaya mata baƙar magana a kansa. Satinsa ɗaya da ƙyar, ya uzzura akan lallai, sai an sallame shi, haka aka sallame su suka koma gida. Cikin ikon Allah, Indabo yayi nasara, bayan faɗi tashi, da shige-shige yayi nasarar samun kujerar ɗan majalisa. Har gida Abbu ya sake zuwa duba Al'amin, sai dai kamar wurin jauhar ya zo, da ita suka ɗan yi hira, ya tashi ya tafi. Hafsa kuwa abun duniya ya hanata sukuni, da ƙyar ta samu Alhaji mu'azzam ya fara saurararta, sai dai yadda yake bin matarsa sau da ƙafa, yake ƙona mata rai, sai abun da ta tsara yake yi a gidan, idan ba ta ga dama ba, sai ya shafe kwana goma bai taka wurin Hafsa ba, amma kuɗi akwai su, komai take buƙata akwai shi, sai dai fa tsakaninta da miji sai an ga dama a bata aro, wataran yana wurin nata ma, za ta kira shi, kuma haka zai tsallaketa ya tafi wurin matarsa, ga yaransa marasa kirki, sun rainata rashin kunya kala-kala. Da ta matsa ma da ƙorafi, ya ce idan ta gaji ta tafi, shi fa duk lokacin da ya zo wurinta, baya gane komai, haƙuri kawai yake yi shi ma, ta ƙyale shi. Ta gaji tayi yaji, Anty ta din ga yi mata masifa, a kan dan me zata dawo gida, sai asirinsu ya tonu, dole ta cigaba da zama har zuwa lokacin da za a samu mafita. Al'amin ya warke sarai, ya cigbaa da harkokin sa, sai dai jauhar kusan kullum tana gargaɗinsa a kan indabo. Gashi ta riƙe masa wuta a kan yin salla a kan lokaci, da yin azkar, har zama tayi ta ciro masa addu'oi na musamman ta rubuta masa su. Ita kanta ta san ikon Allah ne, da ƙarfin addu'a da take yi, da kuma yadda take bin sa da kyautatawa da biyayya, ya sanya take iya sarrfaa Al'amin, har yake jin nauyin aikata wasu abubuwan saboda ita. Da asuba idan ya je salla ya dawo, da kanta take ajiye masa sigari, kara biyu ko uku, ta ce masa ya sha banda shan ƙwaya kuma. Ta jira ya gama sha, yana ƙaurin yana komai, ta naniƙe masa a jikinsa, dan mantar da shi damuwa, kewar kayan shaye-shayen sa. Da daddare suna kwance, ta ce "Master, ka san abun da matar nan tela tayi mini?" Ya ce "A'a" "Wai na cewa matar nan dan Allah, ta koya mini ɗinki, idan ta yarda zan tambaye ka, na din ga zuwa, ta ce mini za ta yi shawara, wai daga baya ta ce mini mijinta ya ce a'a bai yadda na din ga zuwar masa gida ba, ko kara ba ta yi mini ba, duk wahalar da nake yi mata, wani abun ta biyani wani sai dai na yafe kuɗin, na ji haushi dama kuma ba ta zo tayi mini jajen abun da ya same ka ba" "Saboda ni me mijin ya ce bai yadda ki je gidansa ba?" "Wallahi ban sani ba, na dai ji babu daɗi gaskiya, amma ban san dalilinta ba" Al'amin ya ce "Manta da ita, Allah ya baki wani abun da ya fishi, uwar son kuɗi" "To wa ya ƙi kuɗi master" yayi murmushi yana shafa bayanta. Da asuba, mutane sun fito daga masallaci, faruku tela ya ga Al'amin a ƙofar gidan sa. Gabansa ya faɗi ya ce "Lafiya kuwa?" Al'amin ya ce "Saƙonka na ji, 'yar madara ta ce a koya mata ɗinki ka ce a'a, fine idan na kuma ganin 'ya'yanka sun tako mini gida, sai na daddatsa su, na zuba a leda na kawo maka. Na kuma yi suspending ɗin shagonka, na wata guda, wallahi ka buɗe sai an sassara mini kai" yayi tafiyar sa ya bar faruku a wurin, cikin tashin hankali. Ƙarshe sai da aka haɗa da zuwa har gida, magidanta suka zo ban haƙuri, jauhar tayi mamakin abun da yayi, ita kawai hira tayi masa abun miji da mata, amma ya je yana yi wa mutumin barazana. Ta ce zata yi masa magana ba wani abu, malam faruku ya cigaba da buɗe shagonsa. Ya dawo da daddare, ta sha kwalliya, kamar yadda ta kan caccanza tare da ƙirƙiro da sabbin abubuwa, domin sabunta abubuwa da yawa a rayuwar auren na su, saboda rage barazanar gundurar juna. Ya nemi wuri ya zauna a falo, yana ta sauke numfashi, ta fito ta na murmushi ta haye kan cinyarsa, ta zuba masa ido ya lumshe idonsa yana ta huci kamar kumurci. "Nawan" tayi maganar tana shafa sajensa. "Yau kuma me aka sha haka? aka ƙi kulani" yayi shiru bai ce mata komai ba. "Master" "Mmm" "Me ka sha yau?" "Wiwi" Jauhar ta ce "Da me?" Ya girgiza mata kai alamar babu. "Ba ka saba ƙarya ba" ta saka yatsanta a bakinsa, ta ciro guntuwar ƙwayar da take ƙasan harshensa, laɓɓansa sun yi fari. "Ƙwaya ko? Meyasa. Na ce fa idan an ɓata maka rai ne, ko kana cikin damuwa ka yi ta ambaton Allah, kana azkar, meyasa za aje a sha ƙwaya, ka ɓata mini shirina na yau gaba ɗaya" Babu tsammani, ya miƙe da ita a jikinsa, ya tafi da ita ɗakinsa, rabi a buge yake, rabi a cikin hayyacinsa, yayi ƙoƙarin kissing ɗin ta, ta ce "Ba zaka sumbace ni, da sauran ƙwaya a bakinka ba master, me aka yi maka?" "Mhmmm bakomai, i need you" Ta ce "A hakan, a buge fa ka ke" "Ina hayyacina, kin yi mini kyau ne sosai" kasa hana shi tayi, ya gama ya cigaba da yi mata surutai. Ta rungume kansa a ƙirjinta tana shafawa ta ce "Na san wataran zaka daina master, Allah ya shirya mini kai mijina" "Madarata" Ta ce "Idonka biyu" "Mmm" "Me zaka gaya mini?" "In sha Allah zan daina, ki cigaba da yi mini addu'a" yayi maganar cikin muryar maye sama-sama. "Addu'a kullum ina yi maka master, Allah ya nuna mini ka daina" "Madarata" "Master na" Ya ja jikinsa, ya kai bakinsa saitin kunnenta, ta yi shiru, tana jiran ya yi mata magana. Kawai ya fara murmushi, yana yi mata numfashi a kunne. "Zaki koma makaranta" "Allah ya ja zamaninka, godiya nake" Cikin mayen ya sake cewa "Ki daina yawan kuka ba na so" "To ka daina sakani" "Allah ya bani kuɗi na kai ki makka" "Amin Mijina, da alama ƙwayar nan nishaɗi take sawa" "Ke ce nishaɗin nawa" yayi maganar yana dariya. Ita ma murmushin ta yi masa, ya kwanta a gefenta, bacci ya ɗauke shi. Da Asuba ya rigata tashi, ya tasheta shi kuma yayi wanka yayi alwala ya fita. Da wani irin tashin zuciya ta tashi, kamar za ta yi amai, ta danganta hakan da awarar da ta yi wa cin ƙoshi jiya da daddare ulcer ta tayar mata. A ɗakinsa ta yi sallar ta idar, idonta ya sauka a kan robar cocala da ke gefen katifarsa. A take ta ji idan ba ta sha coke ɗin nan ba, akwai matsala. Ta ɗaukko, ta buɗe ta kafa kai ta fara sha, sai da ta shanye tas, sannan ta ajiye jarkar, still ta din ga jin kamar za ta yi amai. Ta yinƙura ta tashi, ta tafi banɗaki, ta yanke jiki ta faɗi, jini ya fara gangarowa daga hancinta. Ayshercool 08081012143 41 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Al'amin a masallaci, magidanta suka tare shi suna ƙara bashi haƙuri, a kan abun da ya ce wa faruku tela. Ya koma gida ya shiga ɗakinsa, yanayin kwanciyar da ya ga jauhar ne ya sanya ya tsaya yana kallonta. "Wace irin kwanciya ce ki ka yi haka, ko baki da lafiya ne?" Ya ga shiru ba ta motsa ba. Ya ƙarasa gabanta, ya ɗagota, gabansa ya faɗi, ganin hancinta na ta zubar da jini, bakinta ma jinin ne yake fita haɗe da wata kumfa. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" ya furta cikin tashin hankali yana jijjiga jauhar. Amma shiru ba ta amsa ba, ya ɗaga hannunta ya ga ya saki, ya kai hannunsa hancinta amma babu alamar numfashi a tare da ita. "Jauhar, meya same ki haka? Meya sameki ne?" Jijjigata yake iya ƙarfin sa, amma ba ta motsa ba, kawai idonsa ya sauka a kan robar cocala. Ya kai hannu ya ɗauka ta shanye komai tas. A wurin Nura guduma ya ƙwace, ganin yadda ya haɗa uban ƙwayoyi a ciki zai sha, ya ƙwace ya ƙare masa zagi, ya ce idan yana wannan haɗin kashe kansa zai yi. Ya taho da shi gida ya ajiye a bayan katifar, ya kai kwana uku a ɗakin, shi ya ma manta da ita a ɗakin. Da sauri ya ɗaukota ya fito da ita falo, ya kwantar da ita, ya fita da gudu, ya rasa wani gidan ma zai dosa, saboda ba shiga harkar mutanen layin yake ba, amma kasancewar a kiɗime yake, ya saka ya nufi gidan wasila, dan maigidan ya sai mota. Wani irin mahaukacin bugu ya din ga yi wa gate ɗin gidan, ba shiri mijin wasila ya fito daga shi sai gajeren wando, ya buɗe yana rarraba ido. "Ɗaukko mota matata babu lafiya" ya ce "To" dan a yanayin fuskar Al'amin ko ba'asi ya tsaya tambaya, bai san me zai yi masa ba. Jin bugun gate ɗin, ya sanya wasu daga maƙwabtan su fitowa, su ji ko lafiya. Mijin Wasila ya fito da mota, yanayin halin da ya fito da jauhar, ya sa gaba ɗaya jikinsu yin sanyi, dan babu alamar rai a tare da ita. Mijin wasila ya ce "Bari ya taso matarsa a tafi da ita, asibitin" Cikin ikon Allah suka yi wa Al'amin kara, mussaman da jauhar tana girmama su da jan yaransu a jiki, maƙwabcin mijin wasila ma ya shiga motar ya ce su tafi tare. Asibitin da ya taɓa kaita aka buɗe mata file suka tafi. Suna tafe yana girgizata yana ta tashi. "Malam Al'amin ka yi haƙuri, ka daina jijjigata kar ka ƙara gajiyar da ita" Al'amin bai bi takansa ba, ya riƙe hannun jauhar, "Dan Allah ko motsi ki yi Zahra, dan Allah ki tashi" su dai duk suka yi shiru, yanayin tashin hankalin da yake ta tattare da Al'amin ya ƙara bayyanar da tsantsar soyayyar da yake yi wa jauhar. Suna zuwa Asibitin, Al'amin ya nufi emergency da ita, sai da aka bishi aka tambaye shi file numbern ta. Mijin wasila ne ya biya kuɗin ganin likita, dan ba ya cikin nutsuwar da za a tambaye shi kuɗi. Likita ya ce "Malam, meyasame ta?" Al'amin ya rasa ta ina zai fara. "Guba ta sha" "Guba kamar yaya? Wannan ma ai kamata yayi sai an zo da 'yan sanda, ya aka yi ta sha guba?" "Ka fara ceto mini ranta, duk wani bayani na yi maka daga baya, ka ceto rayuwar ta tukuna". Likitan ya ce "Ai sai ka fara gaya mini meyafaru?" Ya juya kan jauhar, ya duba pulse ɗin ta, tana bugawa a hankali. Aka samo bandage, aka toshe hancinta, saboda jinin da yake fita, aka ɗagota ƙirjinta a sama a kan gadon. Likitan ya ce "A cire mata hijjabin nan" Al'amin ya riƙe hijjabin, ya yi shiru. Nurse ɗin ta ce "Malam ranta za a ceto, ka yi haƙuri" Mijin wasila ya cewa maƙwabcinsa su fita. Suka fita daga emergency, kayan bacci ne kawai a jikinta, doguwar riga iya gwiwarta. Halin da take ciki, bai hana shi jin matsanancin kishinta ba, likita kuwa aikinsa kawai yake yi, zuƙe jinin da yake bakinta, da kumfar da take fita. Sannan suka fara yi mata CPR, a hankali take ajiyar zuciya, zuciyarta na ƙoƙarin responding. Wasila ta ce "Likita wani jinin na bin ƙafarta" Wani likitan aka kuma kira, aka tafi da ita scanning room, nan suka ga akwai ciki, sai dai shi ma ya fita. Al'amin ya rasa in da zai saka ransa, Nurses suna aikinsu, likitoci na nasu, aka ce Al'amin ya fita ya ce wallahi ba zai fita ba. Haka aka din ga ɗaga jikinta, ana ƙoƙarin tsayar da jinin da yake fita ta ƙasanta, allurai kuwa tsira mata kawai ake yi, ban da wanda ake zuba mata a cannula. Al'amin ya ji da ma shi tsautsayin nan ya faɗawa ba jauhar ba, ko a iya haka ta galabaita. Sakamakon gwajin jini, ya fito jininta ya yi ƙasa matuƙa ana neman a ƙara mata wani. Ya fita hankali a tashe, mijin wasila ya ce "Al'amin ya ake ciki?" Idonsa jawur ya ce "Jini za'a bayar, ku bani aron waya dan Allah, na kira a kawo mini kuɗi, da kuma wanda za su bayar da jinin". Ɗaya maƙwabcin na su hadi ya ce "Ai sun ce sai an yi depositing dubu hamsin za su ganta, mun je reception mun biya, yanzu jinin a fara dubawa a namu, ko za a dace". Ya ce "To, amma a bani aron wayar dai, na yi kira". Walid ya fara kira ya ɗaga da ƙyar ya ce "Maza" "Kana ina ka nemo kuɗi ka zo asibitin da nake kai Ƴar madara cikin hanzari ba ta da lafiya" Tuni Walid ya ware ya ce "Meya same ta?" "Ka zo kawai". "Gani nan" Likitocin suka kira Al'amin, suka zauna da shi suna tambayar sa meyafaru da ita. "Ƙwaya na ajiye a cikin cocacola ta ɗauka ta sha ba ta sani ba" "Kwanakin baya fa, haka nayi ta counselling ɗin ka, a kan ka daina yi mata abun da yake saka jininta ya hau. Yau kuma ka bari ta sha ƙwaya wannan sakaci ne baka kyauta ba, idan ka yi silar rasa yarinyar nan, Allah ba zai barka ba" Al'amin jikinsa yayi sanyi matuƙa. "Ko ka san cewa tana ɗauke da juna biyu? Yanzu dai ciki ya zube babu shi, kuma a shawarce, idan Allah ya bata lafiya, yakamata tayi tsarin iyali, mahaifarta ta sake hutawa, dan ƙwayoyin sun yi wa jininta ƙarfi fiye da kima" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ba zata sake ɗaukar ciki ba kenan?" "A'a zata iya ɗauka, amma a shawarce, mahaifarta ta huta, dan ya yi affecting ɗin mahaifar, akwai buƙatar ta huta kan ta sake wani cikin " Daga shi har jauhar babu wanda ya san da cikin, tsananin son da take yi wa yara, ya sanya ta mayar da boti kamar ɗan da ta haifa, dan ma kwanan nan ya hanata ɗaukko yaran mutane, tayi ta fama da su tana yi musu hidima. Ya tashi jiki babu ƙwari ya fita, su Walid suka ƙaraso Asibitin, a kiɗime suka nufe shi "Mai zamani ina take? Meyafaru?" Bai ɓoye musu komai ba, ya gaya musu. Cikin tashin hankali Walid ya ce "Amma wallahi ɗan kutm..... Ne kai, wane irin hauka ne zai sanya ka ajiye abu in da zata ɗauka ta sha, kuma ba ka gaya mata menene ba? Ka san jikinta ba zai iya ɗaukar abun da yake ciki ba wannan ai hauka ne" "Mai laya" yayi wa Walid tsawa. Sai dai walid ya kuma narka masa ashariya ya ce "Ba za a kiyayeka ɗin ba, idan ka ji haushi ka saka mini ƙarfe, idan ta mutu kai ka yi asara, wannan ai ganganci ne da wauta" Wata irin zuciya ta yinƙuro Al'amin, ya nemi ya huce takaicin sa a kan Walid, amma Walid ma ya hayyayaƙo masa, dan ba ƙaramin mutunta su Juahar take yi ba, yarinyar was very simple and innocent. Security ne suka shigo, suna ƙoƙarin korar su Al'amin, suna nema su tayar da hayaniya a cikin Asibitin. Liti ya kalli security ya ce "ko dai ka ƙyale su, ko abun ya ƙare a kanka" Walid a fusace shi ma yake yi wa Al'amin martani "Saboda ka ga ba ta da baki, iyayenta ba tuhumarka za su yi ba, shi ne zaka yi musu ganganci da rayuwar 'ya, wallahi daga nan gidan su zan je na faɗa, idan ma kashe auren za su yi, su ɗauke 'yar su" Al'amin kawai yayi shiru, dan da makami a jikinsa sai ya yi wa Walid illa. "A ina za a duba jinin?" Yayi maganar yana kallon Al'amin. Yayi masa banza yaƙi magana. "Wallahi sai dai ka fashe, gaskiya ce sai na gaya maka" ya ce "Liti zo mu duba ina ne za a ɗauki jinin". Mijin wasila da suka koma gefe suna kallon sarautar Allah, suka gaya musu in da lab yake. Ba a samu irin jinin Jauhar ba, sai dai sun bayar da jinin su leda biyu, aka tafi da shi babban asibiti, za a canzo da kalar nata jinin. Suka shiga dudduba in da Al'amin ya shiga, aka nuna musu ɗakin da jauhar take. Suka yi sallama suka shiga, an lulluɓe ta da green ɗin bedsheet, idonta a rufe hannunta biyu duka an saka mata ruwa. Al'amin na durƙushe a gaban gadon, ya riƙe hannunta idonsa yayi ja, fuskar jauhar ta yi yellow sosai alamar ƙarancin jini. Walid ya ƙarasa ya dafa kafaɗar Al'amin ya ce "Mai zamani, ka yi sakaci da wauta, amma ka kwantar da hankalinka in sha Allah za ta tashi, ka yi mata addu'a. Ba a samu irin jininta ba, amma mun bayar da jinin za a canzo, likita ya ce a kira ka" Ya miƙe a hankali, suka fito, Walid yana ta cigaba da rarrashin sa, ya ciro kuɗi a aljihunsa ya ce "Wallahi ka ga dubu ɗari da hamsin aka samu, shi ma jarin kaya ne, na ɗebo su kawai, kuɗaɗenmu na hannun mutane, kana ganin za su isa kuwa?" Al'amin ya haɗiye yawu ya ce "Ban sani ba, maƙwabcinmu ya bayar da dubu ɗari, sai a cire a bashi, in gani idan sauran za su isa". Walid ya dafa kafaɗarsa ya ce "Ka yi haƙuri za su isa in sha Allah, yanzu me ake buƙata kuma?" Ya ce "Jinin dai muke jira a saka mata" "To shikenan, zan je na sake lalubawa ko za a samu kuɗi, ka yi haƙuri ka nutsu. Amma dole a sanar da iyayenta" Al'amin ya ce "Wallahi babu wanda ya isa ya rabani da matata, ka ma daina wannan tunanin" "Nima ban ce a rabaku ba, haushi ka bani ne, Allah ya taimake ka, na kiyayi mai zamani" yayi maganar cikin sigar girmamawa ga Al'amin. Al'amin ya daki kafaɗarsa ya ce "Get out" Yayi murmushi suka fita da liti. Mamaki sai da ya kama mutanen da suka gansu suna faɗa ɗazu. Al'amin ya bawa mijin wasila kuɗinsa, amma ya ce kyauta ya biya ba sai an biya shi ba. Babban burin Al'amin bai wuce ya ga ta farka ba, da ya tuna abun da aka ce na game da mahaifarta sai ya ji ya tsani kansa, sai kokowa yake da zuciyarsa yaƙi bari haushin Nura guduma yayi tasiri a zuciyarsa. Wasila ta koma gida, ta dafo musu abinci ta dawo asibitin. Har la'asar Al'amin ya rasa nutsuwa, aka kawo jini aka saka mata. A gigice Nura ya zo asibitin jin abun da ya faru, sai dai ko kallonsa Al'amin ya ƙi yi. Ya rasa in da zai saka kansa, mussaman da ya ga juahar a kwance ana saka mata jini, duk da tsananin kishi irin na Al'amin, Nura yana good time da jauhar, mussaman yake zuwa idan tana da aike, ya karɓa yayi mata, har kasuwa yake zuwar mata, sayen kayan beads da stone work. Ta dafa abinci ta bashi, duk da yaron mijinta ne, kuma tana aikensa, hakan bai hanata girmama shi ba, da yi masa nasiha wasu lokutan. Ganin shi ne sila, a ƙoƙarin hana shi illata lafiyar sa da Al'amin yayi tsautsayi ya faɗa kanta, ya sanya ya koma gefe yana kuka, saboda ya firgita da yanayin da ya ganta kamar gawa. Al'amin cikin tsawa ya ce masa ya fita ya bashi wuri. Nura ya fita wajen ɗakin ya tsaya cikin damuwa. Al'amin ya je gida, ya bar jauhar da wasila, ya je ya yi wanka, ya ɗaukko mata kayan da za a canza mata. Sai bayan sallar magariba ya dawo, ya tarar da Baba tare da mama Anty zakiyya da kuma saifu a ɗakin, wasi ta goge mata jikinta, da taimakon Nurses ta saka mata kaya. Tsayawa yayi yana kallonsu, yana tunanin ma a ina ya san su. Sai daga baya, ya tuna Baba, ya durƙusa ya gaishe shi, ya amsa masa tare da faɗin ya mai jiki. Ya amsa da "Da sauƙi" yana tunanin me Walid ya je ya gaya musu. Baba ya ce "Meyafaru ne? Wani ya je ya ce mana abokinka ne shi, wai ka turo shi an kwantar da jauhar a asibiti, hankalinmu duk ya tashi" Al'amin ya ce "Ɓari ta yi" Anty ta ce "Amma shi ne aka je aka ɗaga mana hankali, ni wallahi na zata wani abun ne ya same ta ma". Mama ta ce "Duk da haka, tun da aka kai ga ƙarin jini tana jin jiki, Allah ya sa ba wani abun ne ya faru ba tayi ɓarin" Al'amin bai ce komai ba, ya ajiye kayan hannun sa, dai-dai lokacin Jauhar tayi wani yinƙuri zata faɗo daga kan gadon tana kiran "Master kana ina?" Cikin hanzari ya ƙarasa gaban gadon, suna rige-rige da shi da Saifu. Yayi hanzarin riƙe ta ya ce "Zahra" "Master" "Na'am sannu" "Meyasame ni ne? Kaina fa zai tarwatse ciwo master" Babu kunya ya rungumeta ya ce "Zai daina, ki daina ɗaga muryarki" Cikin kuka ta ce "Master bana gani, duhu nake gani bana ganinka" tayi maganar tana tittirza ƙafarta a kan gadon. Ya ce "Zaki ganni in sha Allah, ki daina magana" Al'amin ko a jikinsa, ya ttatara hankalinsa a kanta, Baba ya ce "Waliyiyya, sannu kin ji" Ta ce "Baba" "Na'am jauhar" "Baba kai ne ka zo bana ganinku, duhu nake gani, makancewa na yi?" Saifu ya ce "Baki makance ba, bacci ki ke ji, ki yi shiru" "Yaya saifu, bana gani fa" Saifu ya ce "Bacci ki ke ji ne" Cikin fita hayyaci ta ƙanƙame Al'amin ta sake cewa "Master" "Na'am madarata" "Kaina zai fashe, ka riƙe mini shi da ƙarfi, marata ma ciwo take yi mini sosai" tayi maganar numfashinta yana fita sama-sama. Yayi ƙasa da muryarsa yana yi mata raɗa ya ce "Kina jina" ta ɗaga masa kai. "Ki daina magana, ki yi shiru baki da lafiya" "To meyasame ni?" "Zazzaɓi ki ke yi" Ta ce "To, ka je sallar asubar ne?" "Na je mana, har na yi mana addu'a" "To ka riƙe kaina da ƙarfi ka yi mini addu'a, jikina ma kamar an jona mini shocking nake ji" Nurse ɗin da ta shigo ta ce "Malam ya ka ɗagata ana ƙara mata jini, so ake ta kwanta" Mama ta ce "Faɗowa zata yi daga kan gadon, fizge-fizge take yi" Nurse ɗin ta ce "Kwantar da ita, sai ayi mata allurar bacci" Ta rirriƙe Al'amin ta ce "Kar ka ajiyeni, idan na kwanta bana iya numfashi". Al'amin ya ce "To shikenan, ba zan kwantar da ke ba" Anty Zakiyya ta ce "Wannan wane irin ɓari ne, zai saka mutum yayi ta surutai kamar mahaukaci?". Nurse ɗin ta kalleta ta ce "Jini ta zubar sosai da sosai, dan haka jikinta yayi weak, alluran da muke yi mata kuma, sune suke burkita ta, dan haka ba abun mamaki bane ba". Al'amin yayi ajiyar zuciya, jin yadda Nurse ɗin ta rufe musu ainihin abun da ya faru. Ita kuwa tayi hakan ne, dan tausayin yadda tun da ya kawo jauhar yake ɗawainiya, ko da ganganci a lamarin yayi nadama. Sai wurin sha daya suka tashi za su tafi, dan bayan allaurai ƙarancin jini ya saka ta fara haki, athma kuma ta tashi, sai da aka sakata a kan oxygen. Sai dai daga baya ta zama stable, baba ya din ga yi mata addu'a kan su tafi ya ce tsakanin mama ko Anty Zakiyya wani ya kwana da ita Al'amin ya je gida. Al'amin ya ce "A'a baba, zan kwana da ita ba wani abu" dama yanayin fuskarsu ya nuna ba su yi niyya ba. Baba ya din ga yi masa addu'a, sannan suka tafi. Har suka je gida, suna mamakin kulawa da tashin hankalin da suka gani a tatatare da Al'amin. Su Walid ma a reception suka kwana, da an ce a nemo abu, za su fita su sayo, shi kuma yana tare da ita yadda ya ga rana haka ya ga dare. Lokaci -lokaci tayi ta surutu, duk a dalilin mugun ƙarfin da ƙwayoyin suka yi mata. Daf da asuba ta sake farkawa, sai dai ba ta zaburar, wannan karon tana gani, sai dai daga kwance ma jiri take yi. "Master" ya ɗago daga kifa kan da yayi, ya ce "Sannu zahra ya jikin?" "Alhamdilillah, jiri nake ji". "Ki yi haƙuri,  kin ga jini ake ƙara miki. Zaki daina ji in sha Allah, sannu" yayi maganar yana shafa kanta, yana yi wa Allah godiya da ta farfaɗo. Da sassafe Nura ya sake dawowa, har da guzirin bredi da madara da suga, ya dawo sake duba Jauhar, amma al'amin ya kore shi. Liti ne ya dawo da shi ya ce "Haba maza, Nuranka ne fa, waye ba ya kuskure? Kar ka yi masa haka dan Allah, kuma sakacin naka ne ba na sa ba, daka karɓa kamata yayi ka zubar ai, dan Allah ka yi haƙuri" Nura har da kuka ya ce "Dan Allah yaya Aminu ka yi haƙuri, dan Allah wallahi ban ji dadin abun da ya faru ba" Daga kwance ta ce "Master, laifin me ya yi ka ke korar ƙaninka, ayi haƙuri dan Allah, kalli ka saka yana kuka" Al'amin ya ce "Ki daina magana kar hakin ya dawo" "To ka ce masa ka haƙura, ka ga kuka yake yi" A hankali ya furta"Ya wuce" "Yauwwa mai zamani, Allah ya ja zamanin maza" tayi maganar tana ɗaga hannunta da ƙyar ta taɓa fuskarsa. Cikin jin daɗi yadda take ƙarfin hali, yayi murmushi ya ce "Ban hana ba?" Murmushi ta yi masa ba ta ce komai ba. Da nurse ta shigo ta tarar da ita, tana magana, ga su liti a gefe ta ce "Zahra gawa taƙi rami, sannu kin ji" "Yauwwa Anty na gode " Ta kalli Al'amin ta ce "Congratulations, na tayaka muranr farfaɗowarta, dan wallahi mun sare bamu zaci zaki tashi ba" Walid ya ce "Sannunku da ƙoƙari, Allah ya biya ku" "Amin, bari mu gyara mata jikinta, a bata abinci " su liti suka fita, ya taimakawa nurse ɗin, ta gyara jauhar, ta zaunar da ita, duk da tana ta kuka da jiri da ciwon kai da na mara. Ya haɗa mata shayi, da buredi, sai dai ta kasa ci, sai lallaɓata yake yi. Wasila tayi sallama, suka amsa. Ta ce "Alhamdilillah anty jauhar jiki yayi kyau, ikon Allah" Nan suka ƙara gaisawa, ta ajiye abincin da ta zo da shi, jauhar ta ce za ta sha kunun gyaɗar da ta kawo. Ana haka su Baba suka zo, suka tarar da Al'amin yana ba ta abinci an zaunar da ita. Gab ɗaya zamansu a wurin, bai hana shi tattalin matarsa ba, dan gani yake yafi kowa sa'a farfaɗowar da ta yi. Babban abun da ya yi wa jauhar daɗi, bai wuce ganin 'yan gidan su, sun zo dubata ba, ko ba komai sun nuna damuwar su da ita. Duk saifu na ta zuga Baba ya bi diddigin yadda aka yi tayi ɓarin, ko dukanta Al'amin yake yi, amma yanayin yadda suke mu'amala ita da Al'amin ya sanya kowa yin wani tunanin daban, dan saɓanin abun da ake tunani ake gani. Har Abbu sai da ya zo duba jauhar, su shahida ma duk sun zo, Baba sai da ya yi ta yi wa wasila godiya da Addu'a, tana ta ƙoƙari da jauhar, maƙwabtan su ma na ta zuwa dubata. A kwana na uku, da daddare take tambayar Al'amin "Master wai dan Allah meya same ni ne? Na san kawai na ga lemo a ɗakinka na sha, daga nan ban san meyafaru ba, kuma na ji ana cewa nayi ɓari, ya aka yi na yi ɓari ai bani da ciki, ko kuma ina da shi ban sani bane? To yaya aka yi ya zube?" "Ki yi haƙuri, likita zai yi miki bayani in sha Allah" "To kai ka yi mini mana, wai shikenan babyn yanzu babu a cikina" tayi maganar tana shafa cikin ɗauke da damuwa. "Ni likita ne?" "A'a amma ka gaya mini, haryanzu ina da cikin?" Al'amin ya ce "Wai abun da baki san da shi ba ma, zaki bi ki damu, ki yi haƙuri za su yi miki bayani" Ta ce "To shikenan, yi mini addu'a na yi baccin". Ya ce "To" Gari ya waye, su surayya ma suka zo dubata, saifu ya kawo su, take tambayar ina yaya hafsa, aka ce mata ta tafi umara. Jauhar ta ce "Dan Allah ku ce ta yi mini addu'a sosai da ni da master" Suryaya ta ce "Wai ke kowa na gaya wa miji sunan 'yan gayu ke kina master" Tayi murmushi ta ce "Baki ga mastern ne ba? Kuma ai mu ba 'yan gayu bane" Kasancewar Al'amin ba ya ɗakin ya sanya saifu cewa "Ke, ki faɗa mini gaskiya, wani abun yayi miki ko?" Ta ce "A'a me ka gani?" "Wallahi ki ka rufa masa asiri sai kin daku, har likita na saka baba ya tambaya, ko dukanki yayi ya ce babu alamar duka a jikinki da aka kawo ki" Jauhar ta ce "Master ba ya duka, bai taɓa dukana ba". "Na san halinki da shegiyar gwaninta ne, da kare mai laifi ki gaya mini gaskiya" "Wallahi babu abun da ya yi mini" Dawowar Al'amin ya sanya su yin shiru, ya ƙarasa gaban gadonta ya ce "Me zaki ci?" "Bakomai, kawai a sallame ni" Ya zauna a gefen gadon ya ce "Ba na son rigima, wace irin sallama kuma?" "Kai ka koya mini ai, kai fa har guduwa ka ke daga asibiti" Yayi murmushi ya ce "Zaki gudun kenan?" Ita ma murmushin ta yi ta ce "Kashe kuɗin yayi yawa, ina iya tashi ai" Rarrashin ta ya din ga yi, dan shi kansa ya san zaman asibiti da gundura. Sai da ta kwana shida, an saka mata jini ya kai leda biyar, sannn aka fara zancen sallamar ta ranar. Daga likitan sai ita da Al'amin a ɗakin, yayi mata bayanin abun da ya faru, tare da gaya mata akwai buƙatar ta huta kan ta sake ɗaukar ciki. Ya yi wa Al'amin faɗa a kan ya kiyaye sosai da sosai, wannan karon sun rufa masa asiri idan ya ƙara faruwa. Jauhar ta sunkuyar da kai, sai kuka. Likitan ya ce "Menene? Meyafaru? Kuma?" Al'amin ya ce "Bakomai, zamu yi magana da ita" Likitan ya rubuta musu sallama ya fita. Yana fita ya ce " 'yar madara menene kuma?" Shiru ta yi masa ta cigaba da kuka. Duk yadda ya rarrasheta, tayi haƙuri ta ƙi yin magana. Baba ya zo da mota, ya ɗauke su ya kai su gida, ya yi ta yi wa Al'amin godiyar ɗawainiyar da ya yi ta yi da jauhar a asibiti, yayi musu sallama ya tafi. Al'amin ya zauna kusa da jauhar ya ce "Dan Allah ki gaya mini menene?" "Komai ma, kawai ka janyo na rasa babyna, kuma wai ba zan haihu yanzu ba, wataƙila ma ba zan sake haihuwa ba". "Subhanallah kar ki yi mana wannan fatan, zaki kuma haihuwa cewa suka yi kawai ki bayar da tazara saboda yanayin jikinki". Cikin kuka ta ce "Ai da ka daina shan Wannan abubuwan, duk da ba haka ba. Kawai ka ja na yi asara ga jinina ya ƙare, kuma wai ba zan haihu yanzu ba" Cikin tsananin nadama yake rarrashinta, sallamar mutane ya sanya ya tashi, 'yan dubiya suka din ga zuwa duba jauhar. Al'amin na ta hidima da ita, da sassafe yake tashi ya yi aikace-aikace, girki ne kawai sai maƙwabta sun shigo suke yi mata. Shahida ma ta yi ƙoƙari sosai, dan tana zuwa ta taya jauhar aiki, a haka suka saba. Guduma ya sake zuwa har gida ya duba jauhar, tare da gaya mata abun da ya faru. Jauhar tayi masa nasiha sosai a kan shaye-shaye. Al'amin ya fara bata tausayi, har rama yayi sosai, mussaman daina kula shi da tayi, sai yayi ta kame-kame. Yau da ya dawo, normal ta karɓi abun ta. Har ya tafi ya kwanta, ta bishi ɗakinsa. Ta hau gadon ta kwanta ta ce "Master" "Mmm" "Ka yi haƙuri dan Allah, komai ya wuce na ji babu daɗi ne kawai shiyasa kawai" Ya ce "To" "Kayi magana mana, ba to ba" "Ina jin babu daɗi, missing babynki da ki ka yi, ki yi haƙuri laifina ne" "Ba fushi na yi dan cikina ya zube ba, fushi na yi saboda bani ba har kai kana yi mini ganganci da rayuwarka, ka daina dan Allah for our own good and safety" Ya ce "To in sha Allah" "Yaya za a sha fankar ne?" Ya girgiza kai ya ce "Likita ya ce ki huta tukuna kar ki sake ɗaukar ciki". "Sun yi mini allura ai, ko haryanzu ba ka jin komai" Ya ce "Da ɗin ma ina ji, mazewa nake yi, a madadin hakan sai in sha in bugu in manta da ke" "Master nawa nikaɗai, daga ni ba ƙari" "A'a saura uku" Ta ce "To ga fili ga mai doki nan ai" Ya ce "Filin da dokin naki ne ai, ki yi yadda ki ke so madarata" *** Jauhar ba ta samu damar yin jamb ba, saboda rashin lafiya, dan haka Al'amin ya samu indabo ya ce A alƙawarurrukan da ya yi masa, yana son ya samawa jauhar admission, tare da samawa Nura guduma aiki ko na direba ne, a manyan ma'aikatu. Al'amin ya daina shigo da duk wani abu na shaye-shaye gidan, ko zai yi a iya waje yake tsayawa yayi abun sa. Jarin su duk ya ƙare a asibiti, dan haka ya yanke wata shawara a ransa. Ayshercool 08081012143 42 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Jauhar ya fara samu da maganar, da daddare suna tare ya ce "Na ce ba" "Ka ce me ranka ya daɗe?" "Wani abu na yanke ne, ina son na samu Abbu, ya bani gadona na wurin ummi, in sayar da abun da zan sayar na karɓi kuɗi a wurin indabo na haɗa na fara wata sana'ar ina son barin sayar da wiwi gaba ɗaya". Tayi murmushi ta ce "Alhamdilillah, tunani mai kyau, amma ba a yadda ka gaya mini haka zaka je ka gaya wa Abbun ba ko?" "A yaya zan gaya masa?" "Cikin kwantar da murya, zaka yi masa bayani, ka san iyaye sai ana lallaɓa su, ka sani ma ko ya kai ka kasuwa?" Ya ce "Ko ya kai ni ba na so, ya je ya cigaba da riƙe 'ya'yan matar can. Dama alhkina ne ya sa yanzu ba shi da kuɗi kamar da" Jauhar ta ce "Haba master, Abbun ka ke gaya wa haka, kai zaka ji daɗi ka haifi ɗa yayi maka haka?". Cikin ko in kula Al'amin ya ce "Duk tsanani, ba zan yi wa ɗa na abun da yayi mini ba" "Master ka san shiga tsakaninka aka yi da Abbu, dan Allah ka daina irin wannan maganar". Yayi mata shiru, ta sake cewa "Master yaushe zaka kai ni mu gaida su Hajiya?" "Ba rana? Tun bayan kawo ki sun kuma zuwa?" "Hmm master, Allah ya baka damarmaki, duk da ka rasa ummi da yaya sadik, da kuma uban gidanka. Ko yaya dole nan gaba yaranka su so ganin 'yan uwanka, dan da dangin uba ake ado. Ni fa duk wannan abun da ake yi, bani da wayo sanin mahaifiyata ta rasu, ba 'yar gari bace, yar jalingo ce, ba a taɓa kai ni garinsu ba, ba a taɓa nuna mini ko mutum ɗaya a danginta ba, kuma ban taɓa ganin kowa ya zo daga garinsu ba. Da na fuskanci babu uwata a gidan, na nemi ba'asin in da take, baka ga dukan da mama tayi mini ba, ban haƙura ba na tambayi baba, amma ya ce idan na kuma yi masa zancen dangin mamana, sai ya zane ni. Yadda yake nunawa da yadda su mama ke faɗa yana son mamana, amma nayi mamakin yadda yaƙi yadda a kai ni garin su na ga ko 'yan uwanta, da naga ba ya so kawai na daina maganar. Kai kuwa da ka rasa uwa akwai makwafinta, yakamata mu je mu ga hajiya mu gaisheta, ni ba wanda zan kalla na ce daga wurin dangin mahaifiyata yake". Yayi ajiyar zuciya ya ce "Kuma ba ki san a ina take a jalingon ba?" Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, kawai iya abun da na sani kenan" "Shikenan, zamu je mu gaida hajiya, amma sai na tambayi Abbu in da take a tofan ba zan iya tunawa ba" "Yauwwa maigidan Allah dai ya iya maka, ya goyi bayanka yayi maka jagora " Ya shafa fuskarta ya ce "Amin madarata" "Yauwwa milona" Ya ce "Ga madara ga milo, sai Shan shayi" suka yi dariya tare. Washegari da safe bayan sun karya, ya bata magunguna ta sha, tana ta lallaɓa jikinta, za ta yi aikace-aikacenta, ya hanata ya fito ya yi mata share-share, har tsakar gida ya wanke mata. Kayan da ta cire yake wankewa, aka buga ƙofa, ya je ya buɗe hafsa ya gani a tsaye, hannunta riƙe da leda. Ya bata hanya ta shigo, a tsorace ta kalli Al'amin fuskarsa a haɗe ta ce "Ina kwana" "Lafiya ƙalau". "Dan Allah wurin jauhar na zo" da hannu ya nuna mata falo. Daga falon ta ce "Muryar wa nake ji kamar Yaya hafsa" Ta ce "Nice" Ta tashi ta taro hafsa ta ce "Sannu da zuwa". Hafsa ta ce "Yauwwa sannu ya jiki?" "Jiki Alhamdilillah, ya aka yi ki ka gane gidan?" "Yaya saifu ne ya gaya mini hanya, kuma direbana da yayi tambaya aka nuna masa gidan ba wuyar ganewa". Ta ce "Allah sarki yaya hafsa tun ina Asibiti nake tambayar kina ina, aka ce mini kina umara, na ce baki gaya mini ba muna chat, ai da na jero addu'a ayi mana ni da mai gida" Tayi murmushi ta ce "yanzun ma an yi miki, wai jauhar ɓarin da wahala ne, na ga kin rame haka kin yi fari?" "Kai da wahala mana, jini na zubar sosai shiyasa na yi haka, amma kwanaki ai ƙiba na yi sosai, ashe ciki ne ban sani ba" "Allah sarki, Allah ya kawo mai amfani, sannu" "Yauwwa ai na warware " Al'amin ya shigo falon, jauhar ta ce "Master ba ka ganeta ba ne? Yayata ce da muka je gidanta fa, ba ka ga muna kama ba?" Kai tsaye ya ce "Na gani, kin fita kyau" Jauhar ta ce "Kai fa ka fiye son kai ta ina?" "Ta ko ina" yayi maganar yana shigewa ɗakinsa. Hafsa tayi murmushi ta ce "Aikam kin fi mu kyau ai duk gidan nan" Jauhar ta ce "Rabu da shi, shi ma faɗa kawai yayi" suka cigaba da hira, ya sake fitowa ya shirya tsaf zai fita. "To yau me ki ke so? Kayan cikin ko ganyen wanne ki ke so?" Ta shagwaɓe fuska ta ce "Kai" "Ni ki ke so?" Ta ɗaga masa gira tana murmushi. "Aikuwa zaki kwana da yunwa, me ki ke so?" "Komai ka samu na gode" Ya ce "Abun da zai ƙara miki jini aka ce ai" "Jininka zan sha" ta yi maganar tana dariya. Yayi murmushi ya ce "You are not serious, ki yi addu'a Allah ya sa na samu kuɗi, na sayo miki kaza". Hafsa ta ce "Ai ga miya ma na yi miki, da kazar a ciki" Jauhar ta ce "Ashe zaku yi faɗa da master, tun da ki ka riga shi kawo mini kaza" Murmushi ya sake yi, wanda ya bawa hafsa mamaki, take bin su da kallo, gwanin burgewa. Har zai fita ta ce "Master" Ba tare da ya juyo ba ya ce "Kar na yi shaye-shaye da yawa, kar na yi faɗa da kowa, banda rigima da mutane" ta kwashe da dariya ta ce "Au ka haddace ma kenan, addu'a zan yi maka ai, Allah ya iya maka, ya goyi bayanka yayi maka jagora ya wadatamu da halal ya nesanta mu da haram" Ya waiwayo ya ce "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum, 'yar aljannata" ya juya ya tafi. Yana fita Hafsa ta ce "Innalillahi, jauhar dan Allah ya aka yi ki ka canza mutumin nan, dariya fa yake yi miki, kalli yadda yake yi miki, dan Allah jauhara ya ki ka yi ki taimake ni" tayi maganar cikin tsananin damuwa. Jauhar ta ce "Ban fahimci in taimake ki ba yaya hafsa, meyafaru? Wannan ai normal ne tsakanin ma'aurata, kodayeke shi ya koya mini rashin kunya, da ko kallonsa bana iya yi a gaban mutane" Idon hafsa ya cika da hawaye ta ce "Jauhar, wallahi tun da na auri Alhaji mu'azzam hankalina bai kwanta ba, bai taɓa bani awa biyar cikakkiya ba. Sai abun da matarsa take so yake yi, bai tare a ɗakina ba sai da matarsa ta amince. Ga kuɗin yana da su, yana kashe mini ya sakar mini amm ba su nake so ba, kulawarsa nake so da lokacin sa". Juahar ta ce "Yaya hafsa ba fa abun da ki ke kalla a film ne soyyaya ba a ƙasar hausa da wurin mijin bahaushiya, dole ki fara kallon wane irin mutum ne shi, kin ga mijinki mutum ne mai hidindimu da yawa, ba zai yiwu ace kullum yana da lokacinki ba yakamata ki din ga yi masa uzuri" "Uzuri jauhar, yana da lokacin matarsa da yaransa, gaba ɗaya auren ya fita daga kaina, na je na gaya wa anty, wai wallahi na ɗaga maganar nan, sai ta yi mini Allah ya isa, wai zan saka ayi mata dariya, na zama kamar hoto a wurinsa, ko ɗan abun ɗokin nan na amarci, duk fa ban san su ba. Ke da ki ka auri wanda ake yi wa kallon sai a hankali, babu imani da tausyai a zuciyarsa kalli abun da yake yi miki fa. Ni dai dan Allah idna wani malamin ne da ke, ki haɗa ni da shi" Cikin damuwa jauhar ta ce "Yaya hafsa ni wallahi ban san in da ake ganinsu ba ma, canza mutum daga wani abu da baka so zuwa wani, ba abu ne mai sauƙi ba. Kin san ni irin wahala da gwagwarmayar da na sha kafin mu zo wannan matakin kuwa? Da fari nima damun kaina na din ga yi, daga baya na kama addu'a babu dare babu rana, na haɗa da biyyaya da kuma haƙuri. Master mutum ne, kallon da mutane suke yi masa daban, wanda nake yi masa daban, biyayya da addu'a ne suka canza mini shi. Alkhairin da yake yi mini nake kalla kullum, nake yi wa laifukansa uzuri, har gara ke kina da uwa a raye, ni daga ni sai Allah, da na san bani da wata mafita, na bi abun da ƙaddara ta zaɓa mini, na rungumi abuna hannu bibbiyu. Kuma Allah ya shiga lamarina Alhamdilillah, mijina talaka ne, amma ba kowace mace take da ikon da nake da shi a gidan aurena ba. A zahiri shi nake bawa girman, shi ne jagoran amma a baɗini ni ce sitiyarin rayuwarsa, ina fatan kasancewa da shi har aljanna. Ke ma ki nutsu ki gano menene kurakuranki, sai ki gyara". "Ba wani kuskure, ina kyautata zaton asri aka yi mini wallahi " "A'a yaya hafsa, ki daina faɗar haka, ki miƙa wa Allah lamuranki, wallahi zaki ga canji " Duk yadda jauhar ta so nusar da Hafsa muhimmancin haƙuri da juriya, da dagewa a kan addu'a amma taƙi ganewa kuma taƙi yadda. Zuwa azahar ta tafi, ta yi wa jauhar uban farfesun kaji, da abinci, ta kuma ajiye mata kuɗi ta tafi. Har a lokacin ba ta yadda har da hakkin jauhar a abun da yake faruwa da ita ba. Al'amin ne zaune a gaban Abbu, tun da ya gaishe shi, yayi shiru. Abbu ya ce "Ya jikin 'ya ta?" "Da sauƙi" Abbu ya ce "To Alhamdilillah yarinyar kirki, 'yar aljanna Allah ya ƙara mata lafiya, matso ka haɗa shayi ga kayan breakfast nan" Sai da Al'amin ya kalli Abbu, ya girgiza kai ya ce "Na ƙoshi" "Too, yau kai ne ka ƙoshi da abinci kuma?" Ya bashi amsa da "Eh na ci a gida" Abbu ya yi murmushi ya ce "Na manta ne, ashe fa magidanci ne, ya aka yi?". "Sonake a sayar da gadona, zan ja jari, sana'oin da nake yi, ba sa iya riƙe mu sosai, gashi ina so ta koma makaranta, babu isasshen kuɗi a hannuna. Sai kuma ina son ka bani full adress ɗin hajiya, zan kaita ta gaisheta ta matsa a kan haka" Abbu yayi shiru yana ƙarewa Al'amin kallo, duk ya ɗan yi sanyi daga wani rashin mutuncin, babu uwar sumar da yake tarawa da faratan da yake bari zaƙo-zaƙo, gashi yadi ne a jikin sa saɓanin da, da idan bai ga dama ba da 3quater yake yawo da shirt damatsansa a waje, ya wani nutsu sosai. Abunka da uba da ɗa, wani irin shauƙi ya ji yana kama shi, a yadda ya ga tarin sauye-sauye a tattare da Al'amin. "Kai amma 'yar nan tawa ta kyauta, amma wace sana'ar zaka yi?" Al'amin ya ce "Da wurin buga bulo nake so, ko wurin yin buredi, amma ban gaya mata ba tukuna, ban sani ba ko tana da wata shawarar" Abbu ya numfasa ya ce "Kana ji na Al'amin, tsawon shekarun nan, filayenka sun yi daraja sosai da sosai, idan ka bari suka ƙara kwana biyu sai sun fi haka sosai. Ka je ka rubuto business plan ɗin ka kawo mini, tare da list ɗin abun da za ayi mata na makarantar, sai na baka kuɗin, idan Allah ya dafa maka, aka samu cigaba, sai a sayar da ko gona ce a garinsu a ƙara, ka san kana da wasu kadarorin a tofa" Al'amin ya ce "A'a ni ba na son ka yi mini abu, daga baya azo a saka ka din ga yi mini gori, kawai dai a bani wanda na san nawa ne, kuma ma ni na fi son registration nayi mata da kuɗina da kaina, sai na fi alfahari da haka" Abbu ya ce "Gaskiya ne, kamar ba a nan ka zauna kana ce mini, ba ka son auren ba" Al'amin yayi shiru yana basarwa. "Ka rubuto business plan ka kawo mini, zan san abun yi, ka je ku yi shawarar ina jiranka. Gaba ɗaya haushi ya cika Al'amin, kawai ya ji ba shi ne ba zai yi ba, ya ce "Ina ne gidan hajiya a tofa" Abbu ya kwatanta masa, ya tashi ya fita. A waje suka yi karo da Rahila, bai ko kalli in da take ba ya fice. Ta shiga gidan da sauri, ta samu Abbu "Yanzu na ga Aminu ya fita, Allah ya sa ba wani abun ya aikata ba?" Abbu yayi murmushi ya ce "Al'amin ai rigima ta ragu yanzu, duk da wata rigimar ya zo yayi mini ya tafi. Wai gadonsa yake son a bashi, saboda yayi sana'a ya kula da matarsa" gabanta ya faɗi, ɗan kuwa ba ƙaramin harin filayen nan take yi ba, manyan filaye ne awon gwamanti ga gidaje guda uku. Ko da Abbu ya samu karayar arziki bai taɓawa Al'amin su ba. "Wace irin sana'a kuma, wallahi kar a sayar, ba shi da shi a ina ya samu kuɗin sayen leshin dubu tamanin ya bata ta saka, kalli a asibitin da ta kwanta fa na kuɗi, kalli uban kaji da naman da aka kawo gidan nan da salla, duk ba shi da kuɗin yayi haka? Ni ban taɓa zaton zai iya zama soko har haka ba a kan mace wallahi, yanzu saboda kula da itan ne za a sayar da wannan wuraren?" Abbu ya ce "Ba dai nasa bane ba, shi ya ga zai iya ai" Jauhar ta lallaɓa ta cigaba da sana'oin ta, yanzu tana iya aikace-aikacen ta, ta gama aikin, ta idar da sallar magariba, ta ji bugunsa. Ta buɗe ta kalle shi, ta ce "Malam lafiya ka ke yi wa mutane wannan bugun haka?" "Zance na zo" "A me ka zo" Ya ce "Ƙafata" Ta ce "Ko keke ba ka da shi ma?" Ta fito ta zauna a kusa da shi, a kan barandar gidan malam lawan ta ce "To me ka kawo mini " Ya ajiye baƙar leda ya ce "Gata nan gyaɗa ce marau, suyar yau mai zafi" "Ka rasa me zaka kawo mini sai gyaɗa, anya ka na so na din ga fitowa zancen nan" ya saka hannu zai ɗauke ledar, ta riga shi ɗaukewa ta ce "Allah ya shiryeka, Allah master da da kanka a ka bari ka samo matar aure, za a sha wahala kan ka samu" "In ji wa? Farinjini fa zan yi " "A hakan kana muzurai da zare idon? Kan na saba da kai fa na daɗe, tsoro ka ke bani da sosai " Ya ce "To yanzu fa?" "You are my best friend ever, sauƙin kai ne da kai fiye da yadda ka ke tunani, miskilanci ne kawai matsalarka wuyatta na dafa abinci mai daɗi shikenan an wuce wurin " Suka kwashe da dariya tare, a kan barandar gidan, suka cigaba da hira, suna cin gyaɗa, kasancewar a cikin duhu ne, babu wuta, yake ba gaya mata yadda suka yi da Abbu. "To yanzu wanne zaka yi a ciki, wace sana'ar zaka yi?" Ya ce "Rabu da shi, idan muka je ƙauye zan saka a nuna mini gonakin, a sayar da wata na karɓo kuɗina" "A'a kar ka yi haka master " "Haka fa za a yi, wallahi ba zai taimaka mini ba muddin shegiyar matar nan ta sani, ban da ina duba darajar amintar da suka yi da marigayiyya, wallahi da sai na tsinke mata laka" "A'uzibillah, wannan wace irin magana ce?" "Mu bar wannan maganar, ɗaukko key ki rufo gidan mu fita yawo " ta ce to. Ta rufe gida, ya goya ta a babur, suka tafi ya din ga zaga gari da ita, ya kaita gidan su, ya ce ta shiga ta gaisa da baba mintuna goma ta fito, saboda ya lura shi ne kullum yake kiranta a waya, yana tambayarta ya jiki. Baba ya din ga murna, ganin ta warware, baba da kansa ya rakota, suka gaisa da Al'amin, ya yi ta yi musu fatan alkhairi, da fatan samun wani rabon mai amfani jauhar ta yi shiru, shi kuwa ya amsa da Amin. Ba su da wurin zuwa, ya cigaba da zagaye da ita, suna tafe suna shan iska, ya saya mata kayan ciye-ciye, su rake, awara, dafaffen ƙwai kasancewar dama ba iya cin abinci take yi ba. Har wurin sha daya sannan suka koma gida, ya ci abinci. Ganin yana ta kaiwa da komowa tsakanin falo da tsakar gida, bayan sun yi shirin kwanciya, ya sanya ta gane shaye-shaye yake son yi. Ta kalleshi ta ce "Master ka je ka sha, amma kaɗan dan Allah, ba da yawa ba, kar ka bugu" ya ce "To" Ya fita tsakar gida yayi abun sa ya gama, tana jin sa ya shiga ɗakinsa yana wanka, ya fito ya saka turare ya nufo ɗakinta, duk da yana ɗan warin sama-sama amma ƙamshin turaren ya hana warin yin tasiri. "Ba ki yi bacci ba?" Ta ce "Ban yi ba jiranka nake, na san ko na yi sai ka tashe ni" "Allah sarki madarata" yayi maganar yana rungumeta, ya kwanta da ita a jikinsa. "Wace sana'ar ki ke ganin zan fara?" "Ka yi tunanin ko kala uku ce, sai mu yi addu'a Allah ya zaɓa mana mafi alkhairi " Yayi ajiyar zuciya ya ce "Babu laifi" "Masterna, kai zaɓin Allah ne a gare ni, na gode Allah da bai sanya ni cikin masu yi masa butulci ba". Ya ce "Ni ɗin?" Ta jinjina masa kai. Nan ta bashi labarin hafsa, ya ce "Allah ya ƙara, alhakinki ne ai, daga har ke turin jeka ka mutu suka yi mana mussaman ke, Allah ya ƙara" "Master yayata ce fa" "Koma wacece, ai Allah ba ya barin zalunci". "Duk da haka master" "Ni yanzu dan Allah da gaske kina jin daɗi rayuwar da muke yi a haka?" Ta ce "Gaya mini matar da aka taɓa goyawa a tarihi, aka yi tafiyar da aka yi da ita a baya, saboda ba ta da lafiya? Gaya mini matar talakan da ake ajiyewa masu kula da ita? abubuwa da dama da mata suka rasa a gidan aure ni na samu". "To ai wannan duk ba wani abu bane ba a kan wanda ki ka din ga yi mini, dan Allah kina jin daɗin zamanmu a haka? Just recently kin kusa rasa ranki saboda ni?" Ta ce "Ba laifinka bane ba ai" ya yi murmushi cikin jin nishaɗi, yake ƙoƙarin canza hirar zuwa wani abu daban". "Master" "Mmm" "Ban taɓa jin ka ce kana so na ba, ko dai kara kawai ka ke yi mini, saboda halaccin da kake iƙirarin na yi maka?" "Nima baki taɓa gaya mini ba, kuma ina yi a aikace ai, ba dan haka ba, babu wanda ya isa ya saka na zauna da ke ai". Tana dariya ta ce "Sai abinci" "Ki kiyayeni da abincin nan, kina takura mini fa" Ta shafa bayansa cikin shagwaɓa ta ce "Ba ka ce ba" "Me?" "Ka na so na" "Yanzu dai jirani tukuna, na gama caji, koma menene ya biyo baya". "Ba zaka yi cajin ba, sai ka gaya mini" "Yanzu na tashi na yi waje, zan je na yi wanda na saba, na manta komai, yanzu zaɓi ɗaya" "Ni zaka yi wa wayo ko?" "A'a ba wayo zan yi miki ba, zaɓi na baki". Da safe jauhar ta fito falo, ta tarar da Al'amin a kan kujera, ta ce "Master da me ka yi wanka ne a banɗakina?" "Sabulu" "Wanne?" "To ai abubuwan naki ne da yawa, kuma kina bacci kawai na ɗauki na wata roba, na zuba a soso" "Master feminine wash ne fa" Ya kalleta ya ce "Me ke nan?" "Abun kama ruwa ne, dan Allah yayi kama da abun wanka?" Al'amin ya ce "Kai, wallahi tsirfarki tayi yawa, kama ruwan ma, sai an yi masa wani abu, to sai ki din ga rubutawa a jikin robar" Cikin shagwaɓa ta ce "Gaskiya sai ka saya mini wani, dubu uku fa na saya". "Iyee dubu uku, ke fa wasu lokutan kin iya damfara, dubu uku, wannan abun ne dubu uku, car wash ne fa" "Morning fresh ne, wai car wash kuma yasin sai ka biya ni, ina jin daɗin amfani da abuna fa, kai da ba a gyarawa ka din ga lallaɓowa" "A daina gyarawar, a bar mini abuna a haka, ko kuma ki karɓi car wash" "Sai fa ka biyani, wuyatta na soya maka wainar fulawa da zoɓo mai sanyi, sai ka zazzage mini komai na aljihunka" "Ai dama kin saba cin zalina, ki kwashe mini kuɗi" *** Tun sassafe jauhar ta shirya, kasancewar yau za su tafi tofa, gidan Hajiya, duk da ya ce wuni kawai za su yi da yamma su dawo gida, ba ta damu da hakan ba, tun da dai ya amince za su je ɗin. Ta zata tafiyar mai nisa ce sosai ma, sai dai ba su daɗe ba suka isa garin, kwatancen babu wahala, suka isa har gidan Hajiya. Da ta amsa sallamar su ba ta gane su ba, sai daga baya ta gane Al'amin. Cikin hanzari ta tashi tana yi musu sannu da zuwa. "Al'amin, dama zaka tako ka zo in da nake?" "Tun da ke kin watsar da ni ko?" Ta ce "Ba haka bane, ku shigo" "Amarya, ki yi haƙuri ban sake zuwa ba, ina ta fama da ciwon ƙafa, kuma ina tsoron wulaƙancin matar mahaifinka, ko lokacin bikinka, ba ka ga abun da ta din ga yi mana ba, mahaifinka ma haushina yake ji, shiyasa na janye jikina daga gare ku" Jauhar ta ce "A'a hajiya ki yi haƙuri, ai laifin wani ba ya shafar wani, mu dai zamu din ga zuwa muna neman albarka" "Allah sarki, aure mai gyara mutum, yanzu a dalilin auren ya sanya ka zo in da nake" Al'amin ya ce "Eh, ba dan ta matsa ba ba zan zo ba gaskiya, tun da kema ba ƙaunata ki ke yi ba". Jauhar ta ce "Master ya haka kuma?" "Ba ƙarya nayi ba, ki ke zare mini ido" Sai hajiya ta kama kuka, ta ce "Wallahi da gayya ba zan yi haka ba, ina son 'ya ta ina son ku, amma an yi mini iyaka da ku, kusan kullum sai na yi kukan abun da mahaifinku yayi mini a kanku". Jauhar ta ce "Dan Allah hajiya ki yi haƙuri, ki yafe musu, ke ce makwafin uwa a wurinsa dan Allah ki daina kallon abun da suka yi miki". Al'amin ko a jikinsa, dan ita kanta tsohuwar haushinta yake ji, yadda laifin abbu ya shafe su a wurinta. Daga baya kuma cikin hikima, jauhar ta din ga jan su da hira, kasancewar ranar kasuwar garin take ci, har kasuwa suka je sayen ƙwan zabi, Hajiya ta haɗa wa jauhar sha tara ta arziki ta ce ita da jauhar take jikar, shi kuma ya je ya ƙarata. Yayi mata zancen gonakin mahafiyarsa, ta ce masa "Hayarsu ake bayarwa ana noma, duk shekara ana karɓar kuɗin, mahaifinka bai bani damar zama da shi mu yi magana a kan hakkinka ba, amma kuɗinka suna nan ana tara su, ƙanina ne yake ajiyewa, sai dai ya je Lagos yanzu" "Idan ya dawo zan dawo nima" "Allah ya kawo ka lafiya, kuɗi ne masu kauri sosai kam". Sai yamma sosai, sannan suka koma gida. Ana ta kiran sallar magariba sannan suka shiga gida. Da daddare har sun yi shirin kwanciya, Anty zakiyya ta kira jauhar a waya, jauhar ta ɗaga ta ce "Anty lafiya kuwa?" "Ban sani ba, wallahi jauhar ba kya tsoron Allah, kina so ki gama da duniya lafiya kuwa?" Cikin tashin hankali ta ce "Anty me na yi, lafiya?" "Ban sani ba, yadda mugun abun uwarki ya koma kanta, kema da yardar Allah sai naki ya koma kanki". "Anty haryanzu baki gaya mini me nayi ba?" "Asirin da ki ka yi wa hafsa, gashi an dawo da ita gida, tana ta fizge-fizge tana kiran sunanki, wallahi ki gaggauta karya abun da ki ka yi mata, kafin mu gauraya da ni da ke, baƙar annoba kawai" ta kashe wayar. Cikin tashin hankali ta fita falo tana kuka, ta ce "Master" "Yes yaya" Cikin kuka ta ce "Ka tashi ka kaini gida". "Meyafaru a gidan?" "Ka kaini gida kawai, ba zan iya bacci ba, wai an ce ni na yi wa yaya hafsa asiri, wai sai ihu take yi, tana kiran sunana, wallahi ni ban yi mata asiri ba". Tashi yayi zaune ya ce "In ji uban wa?" "Anty ce ta kira ni, dan Allah tashi mu je, wallahi ban yi mata komai ba" tayi maganar tana wani irin kuka. "Na ga alamar sai na taka wa 'yan gidan nan naku burki a kan zaƙewar da suke yi, ba Zamu je yanzu ba, sai da safe, zan je ni su yi mini bayani" Ayshercool 08081012143 43 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin kuka ta ce "Ni dai dan Allah ka tashi mu je, kar ayi mini wani sharrin ina zaune ban sani ba, dan Allah ka tashi mu je" "No ba in da zamu je, sai da safe idan Allah ya kaimu" Kuka ta din ga yi masa, har sai da ta ƙular da shi, ya daka mata tsawa, ya korata ɗaki, daga kuka kuma numfashi ya nemi ya tafi gaba ɗaya, sai da ya ɗaukkota ya fito da ita tsakar gida, ta kwanta ya din ga yi mata fifita. Kusan dai ba su yi baccin kirki ba. Washegari da safe shikaɗai ya karya, hankalinta gaba ɗaya a tashe yake, ta kasa cin abinci, sai wajen goma sannan ya ɗauketa suka tafi gidan. Ita ta fara shiga gidan da sallama, ba kowa a tsakar gidan, duk sun tafi makaranta yaran gidan. A ƙofar falon baba tayi sallama, ya amsa mata ta shiga ta tarar da shi a zaune yana dudduba wasu takardu. "Waliyiyya, lafiya na ganki a yanzu menene?" Kawai ta je gabansa ta zauna tana kuka, hankali a tashe ya dafa kanta ya ce "Menene? Wani abun ne ya haɗa ki da mijin naki? Wani abun yayi miki?" Ta girgiza kai alamar a'a. Mama ta shigo falon, tayi turus, ganin jauhar a gaban baba tana kuka. "Ikon Allah, sakinki yayi ne ko wani abun ne ya faru, ki ke wannan uban kukan haka?" "Yana waje ma" "Yana waje meyafaru?" Gaba ɗaya ta kasa magana. Ya kalli mama ya ce "Tashi tijjani ko saifu, su je su ce masa ya shigo" mama na fita, ya kalleta ya ce "Gaya mini kafin ta dawo" Kasa magana ta yi, da ta buɗe baki za ta yi, sai haki. Mama ta dawo ta zauna, mintuna kaɗan Al'amin ya shigo da sallama, sanye da baƙar jallabiya. Cikin girmamawa ya gaida baba, amma mama ko kallo ba ta ishe shi ba. "Malam Al'amin, meyafaru da iyalin naka ne? Ko wani abun ne ya haɗa ku?" Ya girgiza kai ya ce "A'a, lafiya ƙalau nake zaune da ita, dama na rakota mu zo mu ji ba'asin kiran wayar da aka yi mata ne jiya da daddare, da har ya hanata bacci. Bana son ace na yi wani abu na rashin kyautawa, amma zan iya cewa wannan zai iya zama zuwanta gidan nan na ƙarshe kuma bana buƙatar kowa ya je in da take, in dai har za a cigaba da tafiya a haka". Baba ya ce "Duk me ya yi zafi haka? Baka faɗi meyafaru ba" "Baba kwanaki yayarta ta zo ta dubata, a gidan na fita na bar su ma tare, na manta sunanta, amma wadda ta auri wanda za ta aura da, kwatsam jiya da daddare an kirata a waya, wai waccan ɗin an dawo da ita gida babu lafiya, tana ihu tana kiran sunanta wai ta yi mata asiri, kwana tayi tana wannan koke-koken ba ta bari mun yi baccin kirki ba, wane irin asiri ana zaune ƙalau?" Cikin tsananin ɓacin rai ya ce "Zakiyyan ce ta kira ki, ta ce kin yi wa hafsan asiri?" Ta jinjina masa kai alamar eh. Ya tashi ya fita tsakar gida, yana ƙwalawa zakiyya kira. Mama tayi wani irin mugun murmushi, sannan ta maze ta cigaba da sallalami. Tana mutsutsuka ido ta fito ta ce "Lafiya ka ke yi mini wanan kiran, ka san jiya ba mu yi baccin kirki ba, saboda jikin hafsa". "Yanzu kin kyauta, abun da ki ka yi?" "Na me fa?" "Ɗaukar waya ki kira jauhar, wai ta yi wa hafsa asiri, wannan wace irin magana ce?" "Amma ai ba ƙarya nayi ba, tun da aka kawo ta sunanta kawai take kira ai" Ihun da hafsa take yi ne ya sanya, suka nufi ɗakin gaba ɗaya, ciki har da jauhar. Sai fizge-fizge take yi, tana kiran sunan jauhar. Jauhar ta ce "Yaya gani nan, kin ganni menene" tana jin muryar jauhar ta hau miƙa mata hannu. Ta ƙarasa ta ce "Gani menene, me ya same ki?" "Jauhar, ji nake kamar na fita da gudu, ai ke na gaya miki abun da yake damuna, dan Allah ki gaya musu ko zasu yadda, Anty taƙi fahimta ta, ni a kashe auren nan na huta, bana son kuɗin, bana son auren. Wallahi jauhar an kai wata guda bana iya bacci saboda ɓacin rai kullum sai na sha maganin tari rabin kwalba, nake iya bacci. Bani da nustuwa, babu walwala da kwanciyar hankali yaya zan yi ne? Ta mallake komai, ban ishe shi kallo ba, yanzu kuma ji nake kamar in fita da gudu, kamar ana yagar naman jikina" tayi maganar tana wani irin kuka mai tare da gunji. "Yaya hafsa magnin tari ki ke sha dan ki yi bacci, ai ni ba ki gaya mini ba, shaye-shaye fa ki ka fara kenan" "Ni ki gaya musu a kashe auren nan, ba zan koma ba na gaji" tayi maganar tana buge-buge. Babu kunya Al'amin ya tsallako, ya janye jauhar gefe, saboda kar tayi mata illa. Asirin da zakiyya take gudun tonuwarsa, ya tonu kowa ya gani. Baba ya girgiza kai ya ce "Kowa ya sai rariya, ya san za ta zubar da ruwa, ki tsaya a nema mata magani, wannan abun da take yi babu lalallai wani asiri ne, wataƙila shaye-shayen da take yi ne". "Haba ya zaka ce haka? Wannan surutan da take yi ba fa a hayyacinta take ba, balle a tabattar da abun da ta faɗa gaskiya ne" Al'amin ya ce "Amma ki ka yadda ita take yi mata asiri, count her of this please, kar a ƙar sakata a wannan maganar" Baba ya ce "Al'amin kama hannun matarka ku tafi, in sha Allah hakan ba zata sake faruwa ba" Jauhar kuwa kuka ta din ga yi wiwi, har da roƙon Al'amin ya bari ta zauna, amma ya ƙi ya ce sai dai su tafi gida. Saifu kuwa ya ce "ba dai kuna murna kun cuci marainiya kun aura mata ɗan wiwi ba, kun aurawa taku mai kuɗi, ai ga reshe nan ya juye da mujiya". Jauhar har sai da ta ji haushin Al'amin, na hanata zama a wurin 'yar uwatta. Aka rasa ainihin abun da yake damun hafsa, shaye-shaye ne? Sihirin ne ko aljanu aka kasa gane kanta, wasu lokutan babu magana abinci ma taƙi ci sai kuka, da daddare ta kasa bacci tayi ta koke-koke tana ihu kamar mahaukaciya. Iyaka Alhaji mu'azzam ya zo dubata, ya zube musu uban kuɗi ya tafi. Jauhar ta samu admission a legal, ta fara karanta shari'a law, indabo ne ya bata scholarship, sauran hidimar makaranta kuwa shi yake yi mata. Har keken ɗinki, ya samo mata a irin wanda Indabo yake cewa zai rabawa mata goma, amma ace an bawa mata ɗari, ya ce ba zai bashi ba, sai idan ya yadda za a ɗauki hoton jauhar da keken a saka a social media. Ya ce babu wanda ya isa ya ɗauki hoton matar sa, ya saka a social media, a kan wani keken ɗinki kuma sai an bata. Indabo ya ce wa Al'amin, ya saka yaron da ya ce a samowa aiki a abuja, an samu gurbin direba a wata babbar ma'aikata top 10 na Nigeria, tare da albashi mai tsoka ya ce ya kai takardunsa na sakandare da aka ce yayi. Guduma bakinsa ya ƙi rufuwa, saboda tsantsar farinciki da murna ta gaske, jin zai tafi Abuja aiki, alhalin idan da wanda ya kamata ya tafi, shi oga kwata-kwatan ne. Mahaifiyar Nura, sai da ta zo tun daga garin da take aure, ta zo ta yi wa Al'amin godiya, tare da jauhar, dan Nura duk ya bata labarin irin zaman da suke yi da su. Jauhar ta mayar da hankali a kan karatu sosai, duk da a gefe guda tana yi wa Al'amin magiyar shi ma ya koma makaranta. A kaso ɗari yanzu babu kaso arba'in na shaye-shaye da neman rigima da Al'amin yake yi. Ya shiga ya fita, aka bawa unguwar su sabuwar transformer daga wurin indabo, lokacin da ta su ta lalace, a cewarsa 'yar madara ba ta son zafi. Har burji aka yi wa unguwar aka gyara musu kwatocin layukansu, aka zuba musu burji a manyan hanyoyin su. Abu kamar wasa, sai 'yan unguwar suka fara girmama Al'amin, ganin cigaban da suke samu a dalilin sa, duk da wani abun Indabo ba a son ransa yake yi wa Al'amin ba, dan dai kawai ba shi da yadda zai yi da shi ne. Aka bashi kuɗin sa na garin tofa, na gonakin mahaifiyar sa, kuɗi ne masu yawa, ya yi wa jauhar gyaran gida sosai da sosai, ya canza mata wasu abubuwan, ya saka mata talabijin, dan ma tana hana shi yi mata wasu abubuwan, saboda kar kuɗin su ƙare a banza. Ya buɗe wurin sayar da shayi, a can unguwar su, liti zai din ga kula da wurin, ko Abbu bai san ya buɗe wurin ba. Ta saka shi sun yi addu'a sosai a kan buɗe wurin. Al'amin ya cewa jauhar tafiyar ggagawa ta kama shi zuwa Lagos, juyin duniya ya gaya mata me zai je yi, ya ce mata bakomai, zai je ya duba ne, idan da wani abun da zai iya sayowa ya zo ya sayar a kano. Kafin ya tafi, wasu irin mahaukatan karnuka ya ajiye a layin, su uku masu faɗan tsiya, malam lawan ya tambayi dalilin ajiye wannan karnuka da suke barazana ga rayuwar su. "Tafiya zan yi, gadin mata ta za su yi mini" "Amma banda abun ka, ai Allah ne zai kareta ba karnuka ba" "Meyasa ka gina gida ka saka matrka a ciki, duk da ka san cewa Allah ne zai kare maka ita, ba ka bar ta a titi ba?" Yayi shiru. "Kar ka sake shiga harkat da abun da nake yi na gaya maka" Ita kanta jauhar da fari ba ta ma san saboda ita aka ajiye su ba, ita kanta tsoronsu take ji, gashi sun san lokacin da take dawowa daga makaranta, a bakin titi take tarar da su, da sun ganta, sai biyu su shige gaba, ɗaya kuma yana bin ta a baya. Sai da yayi kwanaki takwas a lagos, sai dai kullum su yi waya amma still bai gaya mata me ya je yi ba. Wurin shayin su liti kuwa, jauhar ita ce yin meatpie, cin-cin, dafaffen ƙwai ne, duk abun da ya samu yi take yi, a lokacin ana processing tafiyar Nura guduma bai tafi ba tukuna, shi yake zuwa ya ɗauka ya kai. Ko ta tsiri yin awara bayan magariba ko wainar fulawa, ya ɗauka ya kai can wurin shayin, kasancewar matasa na taruwa a wurin, sai dai ya kawo mata kuɗinta an saye. Ta ce "Nura ina yi maka murnar tafiyar nan, amma ta wani fannin ni aka yi wa" Ya ce "Wallahi ni kaina na fara kewar ku, na san a can babu abinci mai daɗin naki" Tayi dariya ta ce "Halinka ɗaya da yayan naka ai". Ranar da Al'amin ya dawo kuwa, ta sha tsaraba, har maƙwabta sai da suka samu. Ga kyakykyawar tarba da ya samu daga wurin Uwargida sarautar mata. Hafsa kuwa haka nan aka sasanta, bayan ta ɗan samu sauƙi aka mayar da ita gidan Alhaji mu'azzam, sai dai ba a wani samu sauyi ba, a kan abubuwan da suke faruwa, a baya damuwa da take yi mata yawa ya sanya take shiga tashin hankali, amma tun da ta samu maganin damuwarta ta hanyar shan magunguna masu sanya bacci, sai ta yi overdose yadda za ta bugu sosai ta manta duk wani abu da yake damunta. Dawowar Al'amin ya zo da kuɗaɗe, kuma ya ƙi gaya mata yadda aka yi ya same su. Ba ta zargin sa, dan ta san ba ya taɓa kayan wani, duk abun da zai kai shi ga taɓa abun da ba nasa ba, ba ya ci. Cikin ikon Allah, tun zuwan da suka yi tofa, hajiya take zuwa kawo musu ziyara, da wasu daga dangin mahaifiyar Al'amin. Ana ta shirin tafiyar guduma babban birnin tarayya, ya ce ya fasa ba zai je ba, mahaifiyar sa ta zo har gida ta gaya wa Al'amin, dan bai gaya wa Al'amin cewar ya fasa zuwan ba, mamansa ya je ya gaya wa. Mai unguwa yana ta barbaɗa an yi wa nura hanya zai tafi Abuja aiki. Al'amin ya sa aka nemo masa Nura guduma, ya tambaye shi, menene dalilin sa na fasa tafiya. Ya girgiza kai ya ce "Bakomai" "Ban gane babu komai ba, idan ka zauna a nan ɗin uwar me zaka ci ko ka yi, iyayenka na murna ka samu wurin da zaka rufawa kanka asiri ka ce ba zaka je ba, saboda me?" "Babu komai". A fusace Al'amin"Zan fasa maka kai, ka buɗe baki ka yi mini bayani, meye dalilin da ya sanya lokaci ɗaya ka ce ka fasa tafiya? Duk yaran da suke ƙarƙashina babu wanda na ɗauka na zaɓa sai Kai ka watsa mini ƙasa a ido?" Yayi shiru. "Ba magana nake yi maka ba" "Yaya bakomai" Jauhar ta ce "Master, ka kira shi indabon a waya, ko cire sunansa suka yi? Ko wani abun ne ya faru, tun da ai da murna yake yi zai tafi". Yana huci ya kira wayar indabo, yana ɗagawa ya ce "Yaya aka yi Nura ya ce ya fasa tafiyar nan, ko akwai matsala ne?" Indabo ya ce "Shi zaka tambaya, su kusan bakwai ne, ranar juma'a za su tafi, a kai su wuraren da za su yi aiki, ni ban ma san ya fasa ɗin ba, P.A ne yake kula da shirin tafiyar su". Al'amin ya kashe wayarsa, ya ce "Ba ka da wani dalili ko hujja, dan haka tafiya ranar juma'a " Nura yayi shiru. "Ba magana nake yi maka ba?" Ya ce "To in sha Allah " Bayan tafiyar sa, Jauhar ta ce "Master da ka ƙara matsawa ka bincika, babu yadda za ayi ace da farko yana ɗokin tafiyar nan, lokaci ɗaya kuma ya ce ya fasa, anya babu lauje cikin naɗi?" Ya girgiza kai ya ce "Iskanci ne kawai, maybe abokai suke ziga shi, idan ya tafi can zai zama busy sosai, ba zai samu isasshen lokacin yin rashin ji ba". Ta ce "Eh to, zai iya yiwuwa Allah Ubangiji ya tsare shi, ya sa sanadin shiriyar kenan. To kai ma master a samo maka mana" Ya kalleta ya ce "Wa?" "Kai mana" "Kema kin san ba zan yi ba" Ta ce "Amma ai na ga ba ka raina sana'a komai ƙanƙantarta" "Ba sana'ar na raina ba, ba zan ɗauki duk wani nau'i na rashin mutunci bane, kema kin sani" "Haka ne kam, shiyasa nake mamakin yadda ka ke yi wa indabon nan, yake ƙyaleka, yadda suke wulaƙanta mutane wasu lokutan" Yayi murmushi ya ce "Ni da shi wannan kar ta san kar ne ai" "To ayi amfani da takardunka mana, a samo maka aikin" Ya ce "Ni fa aikin ne ba na so, da zan yi da tun kan maigida dodo ya ware, da na yi, kuma uwa uba yanzu na ajiyeki, yaushe zan iya nesa da ke?" Ta kwantar da murya ta ce "Master nema babu in da ba ya kai mutum, ka taimaka mana" "Ba in da zani, ina maƙale da ke, ga wurin shayi Allah ya dafa mana, wurin bulo ma zamu buɗe, indabo nake jira, shi zai sai injin bugawar" "Ubangiji Allah ya taimaka ya dafa, idan Nura ya tafi, kai zaka din ga kai mini kayan sayarwa ta wurin shayin" Yayi dariya ya ce "Ai idan ma cewa ki ka yi na sayar miki zan sayar madarata, balle kuma kaiwa kawai. "Sannu mijin ta ce" "Bakomai, normal ne" suka cigaba da hira cikin nishaɗi. Al'amin ya tattara Nura sai da ya tafi, Jauhar kuma haki ya addaba mata, wasu lokutan tana makaranta, za a kira Al'amin ace masa an kai ta Asibiti babu lafiya. Sati ba ya zuwa ya shafe, asma ba ta tayar mata ba, kusan kullum suna hanyar asibiti, har ta fara tsoron kar ya fara gajiya. Sai dai sam ba ta ganin alamar gajiyawa, ko ƙosawa a tattare da shi. Ga jiri ga haki, abinci ma gagararta ci yake yi, ga ciwon mara da ya sakata a gaba, period ɗin ya ƙi zuwa sai kaɗan ta gani a phant. S uka sake komawa Asibiti, aka tabattar da ƙarancin jini a tare da ita. Likitan ya ce "Zahra, kina cin abinci ki ƙoshi kuwa?" Ta ce "Sosai ma, master yana ƙoƙari a wannan ɓangaren" Ya ce "To ai ba kowane irin abinci ne ya dace da ke ba, kin manta rashin lafiyar da ki ka yi, da irin abincin da muka ce ki din ga ci". Juahar ta ce "Wallahi Alhamdilillah, dai-dai gwargwado yana bani, duk abun da nake so, ko ba na so ma yana sayo mini" Al'amin ya ce "Ka ga likita, da dai idan na sayo tana ci, amma yan, kwanakin nan, zaɓe-zaɓen abinci take yi, ba komai take ci ba". Likita ya ce "Ayi gwajin ciki gaskiya" Jauhar ta ce "Ai ka ce ayi mini allurar tsarin iyali, an yi mini kuma " Ya ce "Guda nawa?" "Ɗaya aka yi mini, an ce in dawo ta biyun, amma na ji an ce idan baka period ba ta sake ka ba, to period ɗin ma so yake ya zo, amma yaƙi zuwa sai wahalar da ni yake" Ya ce "A nan asibitin aka gaya miki?" Ta ce "A'a" Yayi rubutu ya ce su je ayi scanning. Suka je suka yi, suka dawo, ya karɓa ya duba, ya ce  "Ikon Allah, to akwai ciki, kuma jinin da yake zuba alamu ne na akwai tangarɗa da yiwuwar ya zube idan ba a ɗauki mataki ba" Al'amin ya rasa me zai yi, murna ko kuwa. "To amma likita kana ganin babu matsala, tun da kun ce kar ta ɗauki ciki, a nan kusa bai fi watanni biyar ba yanzu" "Eh, zamu bar ta a ƙarƙashin kulawar mu, in Allah ya yarda babu matsala, yanzu haka ya fara alamun zai fita, tun da ta fara zubar da jini, dan haka muna buƙatar ta samu bedrest, na sati guda daga ci sai bacci, ban da aikin wahala". Cikin damuwa ta ce "Ko a hankali ba zan yi ba" "A'a ba zaki yi ba" "Amma master ka san ba wanda zai zo ya zauna da ni yayi mini fa" Al'amin ya ce "Ni zaman me nake yi?" Doctor Khalid ya ce "Allah dai ya bar wannan ƙauna, sannan kai master kana ji na" "A'a fa, wannan sunan ba kowa yake faɗa ba, kira ni da Al'amin ɗina" Yayi murmushi ya ce "Bedrest ɗin da muka ba ta har da kai a ciki" Ya ce "Kamar yaya kenan?". Doctor ya ce "Ba zuwa turaka" "Meye turaka?" Cikin jin kunya jauhar ta ce "Idan mun je gida zan gaya maka" "A'a ai ba sai kun je gida ba, bayani zan yi masa yana sane ai, babu kai ba ita zuwa mu ga abun da Allah zai yi, ba cikakken hutu ake so ta samu" Al'amin yayi shiru yana kaɗa ƙafa. "Ina magana ka yi banza, idan ka na son babyn ya rayu lafiya kenan, ba tare da an samu matsala ba, idan kuma ka ƙi ba ruwana" "Ai ni sai abun da Allah ya yi ne ban gane ba, nan da yaushe ka ke nufi ne?" "Zuwa cikin yayi ƙwari mana" "To" ya amsa a taƙaice. Doctor ya ce "Ba ka yadda ba kenan?" "Na yadda mana, sallame mu na mayar da ita gida, rana tana yi" Doctor Khalid yayi counseling ɗin su sosai, sannan suka tafi gida, Allah ya taimaketa a cikin hutu suke a makaranta. Sai dai ba a rufa sati da zuwan su Asibiti ba, laulayi ya saka jauhar a gaba, komai ta ci sai ta yi amansa, duk ta rame, har abun ya fara damun Al'amin, yake ganin kamar ɗaukar cikin da tayi da wuri ne, ya sanya take shan wahala har haka. Babu tsammani Abbu ya zo gidansu da daddare, sun yi mamaki sosai da sosai. Bayan sun karɓe shi ya ce "Al'amin ina can ina jiranka, ka kai mini business plan, in ga abun da yakamata na taimaka maka, ashe ka zagaye ka je wurin kakarka ka karɓi kuɗi har ka buɗe wurin sayar da shayi". "Eh, na san ko na rubuta, matarka ba zata bari ka bani ba" Jauhar ta ce "Abbu dan Allah ka yi haƙuri, bai kamata a ƙi gaya maka ba, dan Allah ka yi haƙuri mun yi kuskure" Al'amin ya ce "A'a ni ne ban gaya maka ba, ta ce a gaya maka na ce a'a, saboda ba na son matar nan ta din ga saka mini baki, a abun da ya shafe ni" Abbu ya girgiza kai ya ce "Jauhar ba ki yi laifin komai ba, ni yabo da godiya na zo takanas na yi miki, rayuwar Al'amin ta canza sosai da sosai, fiye da yadda nake tsammani, da na san aure zai katange shi daga wasu laifuffukan da tuni na yi masa an wuce wurin. Allah ya saka miki da alkhairi. Duk da daga baya na samu labarin yadda aka yi, aka zo ga gaɓar aurenki da shi, amma ki ka yi haƙuri ki ka zauna da shi a yadda yake, ki ka din ga gwagwarmaya, a gaskiya ina ƙara yaba miki, Allah ya yi miki albarka ya sa ki gama da duniya lafiya" Jauhar ta ce "Babu komai Abbu, da na yi watsi da shi nima, kamar yadda sauran al'umma suka yi, da ba a samu Wannan nasarar ba" "Haka ne, kai kuma" yayi maganar yana kallon Al'amin. "Ka ji tsoron Allah, a zaman da ka ke yi da yarinyar nan, kana ganin duk wata masifa da kake ɗaukkowa babu mai tsayuwa a kanka, sai ita sai abokan shashancin ka, kai kanka ka san yanzu rayuwarka ta canza ba kamar da ba. Duk rintsi duk wuya, ka rayu da yarinyar nan da mutuntawa da girmamawa, idan ka sake ka cutar da ita, ko wani abu mara daɗi ya faru da ita a dalilinka, to ni da kai sai dai kowa ya kama gabansa". "A'a Abbu ba za ayi haka ba, yana iya ƙoƙarin sa, babu wani abu da yake yi mini ma na rashin kyautawa, ni yanzu roƙo ɗaya nake da shi Abbu, dan Allah ka janye maganar a dalilinsa a ka kashe ɗan uwansa, kuma ka saka baki a kan yayi haƙuri da batun ɗaukar fansar da zai yi a kan madakin nan, tun da ya fita sabgarsa ya zauna lafiya kwana biyu, hankalinmu a kwance" Aikuwa Al'amin ya haɗe rai, Abbu ya ce "Ka ji abun da matarka ta ce, ka yi mata wannan alfarmar da ta nema, kuma nima na nema" "Tom" kawai ya faɗa a taƙaice. Abbu ya din ga saka musu albarka ya tashi ya fita. "Ban yi miki alƙawarin kawo ƙarshen gaba ta da madaki ba, har sai ranar da na tabattar na daina jin ɗanɗanon baƙin cikin, abun da ya yi mini" Cikin kwantar da murya ta ce "To ka bi ta hanyar da ta dace ta shari'a, ba ta makami da illata junanku ba dan Allah" "Ta in da aka hau, ta nan ake sauka" ya bata amsa. Ta fuskanci muddin tana son ganin ɓacin ransa, to tayi masa maganar madaki. Washegari hafsa ta kirta a waya, ta ce "Kwana biyu bana ganinki a online, ko ba data ne matar master?" Jauhar ta yi dariya ta ce "Wallahi akwai data, kawai bana jin daɗi ne, wayar ma ba iya taɓa ta nake yi ba, ya jikinki kuwa?" Ta ce 'Hmmm jiki gani nan dai, ko dai ciki ne kin ce ba kya jin daɗi?" Tayi murmushi ta ce "Ba wani ciki, jikin ne dai kawai". "Bari zan wuce ta unguwar taku, sai na tsaya mu gaisa, me zan taho miki da shi?" "Babu komai, ke dai Allah ya kawo ki lafiya". Bai fi awa biyu ba, sai ga hafsa, sai dai yanayin da jauhar ta ganta bai yi mata daɗi ba. "Yaya, wannan shigar fa kamar ba matar aure ba? Hafsa ta ce "Taɓ, matar aure ai na ajiye aure a gefe, mafita nake nemawa kaina" "Ban gane ba" "Wanda yakamata na yi wa ya gani, bai damu da ni ba, ya haɗa kan matarsa da yaransa sun tafi dubai, sun bar ni ga kuɗi ga gida, nayi-nayi anty ta fahimce ni a raba auren nan, taƙi har tana nema tayi mini baki, zan cigaba da ba ta kuɗi, nima kuma zan nemawa kaina mafita" "A'a yaya, wallahi gara ki kai ƙara hisba a kashe auren, da ki yi zina da aure, ko a sasanta ku ayi masa nasiha". Ta girgiza kai ta ce "Mama tayi mini asiri, banda wanda matarsa take yi mini. Gaba ɗaya ba na gabansa, duk sai na yi maganinsu, daga nan har chadd ko zan tafi tsirara, su surayya ba zasu auru ba, kuma sai na kashe auren nan, ba zan iya ba. Kar ki damu da sai kin yi mini nasiha, dan ba zan ji ba wallahi. Kin ga bari na hanzarta zan je na karɓo kayan cajina a wurin wanda nake karɓa. Ke ni ko da mastern naki zaki haɗa ni ne, ya din ga bani kayan " Jauhar ta girgiza kai cikin matsananciyar damuwa ta ce "Ki dai canza tunani yaya hafsa, ni master na yi nasara a kansa, da addu'a da haƙura, abun da yake yi ya kusa zama tarihi, ke ma da zaki yi haƙu...... "Kin ga tafiyata jauhar, ga farfesun kifi nan da doya, ki samu ki ci, sai anjima". Abun duniya ya ishi jauhar, dan sai da ta zubar da hawaye, ta ɗauki waya ta kira Baba, suka gaisa ya tambayeta ya makaranta ya mijin naki, ta ce "Lafiya ƙalau Baba, dama wani abu ne ya saka na kiraka". "To waliyiyya, Allah ya sa lafiya" "Baba dan Allah ka shiga lamarin auren yaya hafsa ka saka baki, kar abun da ba a so ya afku, yanzu ta bar gidan nan ni dai ina jin tsoro, dan Allah baba ka saka baki" "Waliyiyya kina ji na?" "Eh baba" "Duk Wanda ya ce ;zai haɗiyi gatari, sai ka sakar masa ƙota. Babu yadda ban yi ba, idan auren nan ba zai yiwu ba, a raba uwatta taƙi, na zauna da shi mijin, ya ce shi ba ta da cikakkiyar lafiya, kuma ba ta da kunya, uwatta ta tsaya a fuskanci menene matsalar, tun da ta saka son abun duniya a gabanta, amma taƙi. Ta ce wai asiri babar tijjani tayi mata, suna nan suka ta faɗace-faɗace, kuma na san duk hakkinki ne, ni na zubawa sarautar Allah ido". "A'a baba, dan Allah kar ka ce haka, kada laifinsu ya shafeta, su matanka ne, ita kuma 'yar ka ce, hafsa fa ta cigaba da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi baba ka yi wani abu a kai". Ya girgiza kai ya ce "Jauhar kenan, zan yi ki yi mata addu'a Allah ya shiryeta" Suka yi sallama ta ajiye wayar cikin matsananciyar damuwa. Al'amin ya dawo gidan yana mitar kwana biyu lambar guduma ba ta shiga sam, yana ta kiransa a kan idan an yi musu albashi, ya gaya turo da kuɗi a yi wa iyayensa sayayya, ya basu na neman albarka. Amma shiru lambar ba ta shiga, ya kira P.A ya tambaye shi ya kasa samun sa. P.A ya ce masa suna nan ƙalau yana can yana aikinsa, yana zaton ko wayar ce ta samu matsala. Haka kawai Al'amin ya ji bai amince ba. Ayshercool 08081012143 44 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Gaba ɗaya ya kasa samun nutsuwa sai da jauhar ta farga ta ce "Master ya ne?" "Na kasa samun Nura a waya" Ta ce "Allah sarki, ɗan uwa nagari in sha Allah zaka same shi, maybe ko babu caji ne a wayar" Ya ce "No, kusan sati fa kenan, na kira P.A ya ce mini suna nan lafiya, wataƙila wayarsa ce ta samu matsala, idan ma haka ne, ai ko wayar wani ya ara ya kira ni, tun da kusan kullum sai na yi waya da shi, na ja masa kunne" Jauhar ta ce "Haka ne, amma ƙara masa kwana biyu mu gani" Jiki a sanyaye ya ce "To shikenan" Al'amin ya hana jauhar duk wani aikin wahala, su halimatu ne ke zuwa ta yi guiding ɗin su, su yi mata snacks ɗin da ake kai wa wurin shayi, sai bead work da take yi tana daga zaune, shi ma faɗa yake yi yana mita. Iya haƙuri da ɗaga ƙafa ta san yayi mata, dan yau sakata yayi a gaba yana mita, ba dan yana son cikin nan ba, da tuni ya daɗe da bin rariya shi ma. "Master" ya ɗaga kai ya kalleta, ya haɗe rai. "Wai laifin me na yi ne?" "Ni gaskiya na gaji, sai yaushe cikin zai gama ƙwari ne? Nima ai yakamata a duba lamarina" Murmushi ta yi, yadda yayi kicin-kicin, kamar wani ƙaramin yaro. "Lamba nawa ake so?" Tayi maganar tana kashe masa ido. "Na gaji da lamba uku huɗu, lamba ɗaya nake so" Jauhar ta ce "Baka damu da babyn nan ba ko?" Ya girgiza kai ya ce "Wallahi na damu da shi, ina son abuna, amma ba shikaɗai yake buƙatar ya rayu ba, kuma ba shikaɗai yake buƙatar ki ba" yayi maganar a marairaice. Ta ɗan yi shiru tana nazarinsa, da gaskiyar sa, kusan kullum ba ta da lafiya, tana kallo wasu lokutan sai dai yayi zamansa a ɗakinsa, ya busa hayaƙi, dan kar ya takura mata, ko ya karya dokar da aka saka saboda cikin. "Kin yi shiru fa" Dariya ta yi ta ce "Subhanallah, master da shagwaɓa, lamari ya ɓaci, to lallaɓani". "Ai lallaɓakin nake yi" "Inyee dama ka iya shagwaɓa baka taɓa yi mini ba, yanzu da da safe zan ce ka yi mini mazewa zaka yi kana hararata. To daga yau mayar maka da fankarka zan yi, dama ta fara tsufa". Al'amin ya ce "Zan yi zuciya fa" Ta ce "To yi mana idan zaka iya, huta roro waken gizo yaƙi 'ya'ya" tayi maganar tana jan dogon hancinsa. "A'a ba zan yi ba ma" Tayi murmushi tare da rungume shi. Har suka kwanta tana lafiya, sai cikin dare ya farka ya ganta a zaune, ta takure wuri guda. "Madarata, ya aka yi ne?" Jauhar ta ce "Bakomai, zafi ne ya dame ni" "Zafi kuma? Ga fanka na yi?. Ko numfashin ne?" Ta ce "A'a, lafiya ƙalau nake numfashina" Ya ce "To ya aka yi na ganki a zaune?" Tausayinsa ya kamata, har istigfari take yi, ta gaji da ce masa ba ta da lafiya ba yau ba gobe. "Master ka kwanta dan Allah, na kasa baccin ne" Cikin damuwa ya ce "Ka kwanta ka yi baccinka" "A'a ban yadda ba, akwai matsala ne, gaya mini?" "Marata ce take ciwo" Cikin tashin hankali ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ya sa ba zubewa zai yi ba, ya salam" Ta jingina da jikinsa ta ce "Ciwon fa ba mai damu bane ba, ƙullewa tayi, na ji kwanciyar babu daɗi, shiyasa na tashi zaune" "Ko asibiti zamu je? Wallahi ina son cikin nan zahra, na kwaɗaitu da son ganin abun da zaki haifa mini, tun da muka rasa na farko, nake tunanin ko yaushe zamu kuma samu? Kuma mun samu wannan karon ma, zan yi dalilinsa, mu je asibiti kawai". Cikin sigar rarrashi ta ce "Master, dan Allah kar ka ɗaga hankalinka, ba ciwo take yi mini ba, ƙullewa tayi ne sosai kuma na duba babu abun da yake fita. Ɗawainiyar da ka ke yi da ni ka da Allah ya gajiyar da kai, Ubangiji Allah ya nuna mini ka daina komai kan Allah ya kawo mana babynmu" Yayi ajiyar zuciya ya ɗora hannunsa a mararta ya ce "Ba zan taɓa gajiya da duk wani abu da ya jiɓance ki ba, ba alfahari nake yi miki ba, ɗan halak ne ni, kar ki taɓa sakawa ranki zan gaji, da ƙarfin ikon Allah ba zan gaji ba, in sha Allah, ni dai duk abun da ki ka ji na ciwo ki gaya mini dan Allah, ina son kasancewa da ke da iya adadin abun da zaki haifa mini, mu yi rayuwa mai tsayi da daɗi. In sha Allah zan yi iya ƙoƙarina na zama uban kirki ga 'ya'yana, kuma miji abun alfahari gareki" Haka kurum ta ji jikinta yayi sanyi, da maganganun sa, ji take kamar akwai wani abu mai girma da zai faru da su, sai dai ba ta sani ba, na daɗi ne ko akasin haka. Ta sake lafewa a jikinsa, tana jin tsananin buƙatuwar son cigaba da kasancewa da shi a cikin rayuwarta, ita wannan kulawar da yake yi mata, tana shafe dukkan sauran abubuwan da yake aikatawa. Zuwa da safe ta ji ƙwarin jikinta, har ta ce masa zata makaranta, da ƙyar ya amince, saboda tana da test. Har ta fito ya karɓi jakarta, ya ce shi zai kai ta, kar ta hau ɗan sahu, ayi ta gargada da ita. Ya duba jakar ya ce "Ina inhaler ki?" Ta ce "Tana aljihun wandona" "Meyasa ba zaki saka a jaka ba" "Zai iya yiwuwa ciwon ya tayar mini, jakar tana nesa da ni, amma a wandona da na laluba zan ji ta" "Allah ya baki ingantacciyar lafiya, ya rabaki da ciwon nan gaba ɗaya" Ta ce "Amin bugun zuciyata" Ya ce "Iyeeee?" Ta jinjina kai ta ce "Eh mana" "To bani da kuɗi dai, kayan abinci zan sayo mana, idan kuma na ɗauka na baki shikenan" Ta tsuke fuska ta ce "Kai ba ayi maka abun arziki, da na yi maka kalamai, sai ka hau ce mini ba ka da kuɗi, me ka ke nufi" Al'amin ya ce "Ai ke ɗin ce, wasu lokutan haka ki ke yi mini, bana sanin lokacin da ki ke sakawa na zazzage miki aljihuna" Jauhar ta tura baki ta ce "Wannan kalaman wataran da kuɗi ba zaka ji su daga bakina ba" Take jikinsa yayi shock ya ce "Ban da irin wannan wasan" idonsa ya nuna ƙarara tsananin fargabar rasata. Ta basar da zancen, ya kaita makaranta. Abu kamar wasa, sama da kwanaki biyar, Al'amin bai ji ɗuriyar Nura ba, bai kuma same shi a waya ba, dan haka ya wanke ƙafa ya tafi gidan indabo, kasancewar ba shi da shamaki da gidan, babu mai tambayarsa wurin wa ya zo, ina za shi, kai tsaye ya shige. Ofishin indabo na gidan ya tafi, kasancewar imdabon yana Abuja, cikin sa'a ya tarar da P.A. "Mai zamani, ya aka yi ne?" "Na kasa samun Nura a waya" "To ai ina zaton wayarsa ta samu matsala ne kamar yadda na gaya maka" Ya girgiza kai ya ce "Ba zai yiwu ba, shirun yayi yawa. Ba zai yiwu na baku amanar yaro, garin da ba uwar sa babu ubansa na kasa samunsa a waya, kusan sati biyu, na zauna na yi shiru ba, ba zai yiwu ba, dole ka san duk yadda zaka yi ka haɗa ni da shi" "Amma mai zamani ina nan yana Abuja, a ina zan iya haɗaka da shi?" Cikin ɗaga murya ya ce "Ka kira indabon, duk yadda zai yi ya haɗani da shi" P.A ya tsaya yana kallon sa. "Zaka yi abun da na ce, ko sai na saka maka ƙarfe?" Ya janyo waya ya kira Indabo, suka gama magana. Ya kalli Al'amin ya ce "mun yi magana da honorable, ya ce in anjima zai aika a duba shi, yanzu suna meeting da shugaban ƙasa". Yayi ƙwafa ya juya zai fita, Abdul ya kawo kai shi ma ya shigo. Sai dai Abdul ya tsaya yana jiran Al'amin ya bashi hanya, wannan ce haɗuwar su ta biyu, kasancewar ba a ƙasar yake zaune ba, ya fi sanin ɗayan wato Ja'afar. Ala'amin bai tsaya jira ba, ya yi wa Abdul wata muguwar bangaza da kafaɗarsa, sai da ya dangana da faɗuwa ƙasa. A fusace ya miƙe zai bi bayansa, P.A da sauri ya tsare shi ya ce "Kul, sai ya yi maka illa, ba mutunci ya cika ba wasu lokutan" A fusace Abdul ya ce "Mahaukaci ne shi, baka ba ka ga irin bangazar da ya yi mini bane?" "Yi haƙuri, ai duk abun da ka ga honorable yana bi a sannu, ka san ba ƙarami bane ba, yi haƙuri". Ya kalli P.A ya ce "Babu ruwana za abun da yake bi a sannu, wallahi muka sake haɗuwa sai na koya masa hankali" ya juya ya fasa yin abun da zai yi. Har la'asar Al'amin yana kallon wayarsa, yana jiran kiran indabo, ya je wurin shayi, komai yana tafiya dai-dai, ya tafi gida. Yayi jajjage ya feraye doya, ya dafa ruwa ya zuzzuba a flask, duk ya rage wa jauhar aiki. Wayarsa ta fara ringing, ya ɗaga ya kara a kunnensa. Muryar Nura yaji ƙasa-ƙasa ya ce "Yaya" "Kai Nura wani irin shirme ne zaka kashe waya, ko ta wani ba zaka ara ba ka kirani, ina ta tunanin meyafaru da kai?" Nura ya ce "Ka yi haƙuri dan Allah" "Ya ake ciki? Na ji muryarka wani iri?" Nura ya ja numfashi ya ce "Zazzaɓi ne yake damuna, sun bani hutu ma, an kai ni asibiti an bani magunguna ma" "Yasalam, kai daga zuwa garin mutane sai rashin lafiya, ko aikin ne da wahala?" Ya ce "A'a" "To Allah ya sauwwaƙe, zan cigaba da kiranka, idan ka ga babu hali, kawai ka dawo gida" Nura ya ce "Godiya nake, Allah ya kiyaye ka ya ƙara tsawon zamaninka" "Ka huta, ka kula sosai duk yadda ake ciki, ka sanar mini, ina fatan sun sallameka, dan na ga wata ya ƙare" "Eh an bani kuɗi masu yawa ma, ka bani account number ɗinka, na sako maka abun da na samu, amma a ciki a sayawa Antynmu turimin atamfa dan Allah, da ita da babata a sai musu iri ɗaya" Al'amin ya ce "A'a, ta gode sosai, amma ba haka za ayi ba, ka ba wa maman abun da zaka bata, ka tallafawa babanka da wani abun ya sai kayan abinci" Nura ya ce "Shikenan, tun da ka ce haka, amma dan Allah ka saya musu atamfa iri ɗaya da mamanmu, tana sonta sosai " Al'amin ya ce "Zan duba na ga abun yi, ka kula da shan magani ka ji ko?" "In sha Allah" "Good boy, sai anjima" ya kashe wayar, sai ya ji wata irin sa'aida a zuciyarsa jin muryar nura, dan babu irin saƙe-saƙen da bai yi a kansa ba. Da jauhar ta dawo, aikin gida ƙarashe ne, duk yayi, sai godiya take yi masa tana yi masa addu'a. Jauhar tun da cikinta ya fara tasawa, da an buga gate, sai ta saka hijjabi tana ɓoyewa, wai kunya take ji. Yayi ta yi mata dariya, ya ce "Da ki ɓoye, da ki bar shi, ƙarewa haifarsa zaki yi ƙarshen kunya, gara ma ki bar shi kowa ya gani". Cikin shagwaɓa ta ce "Ni dai ka bari na ɓoye abuna" Ya ce "Ai sai ki yi ta yi" Al'amin ya sha mamaki kuɗin da guduma ya turo masa, dubu ɗari da hamsin, wai a bawa babansa dubu ashirin kawai, sauran har da su oga liti da oga walid ya ce duk rarraba musu. Al'amin ya ce "Wai aikin direban ne aka baka wannan kuɗaɗen har haka?". "Eh Oga, ka san birnin tarayya ne nan, kuɗi ba wahala suke yi musu ba, ka cigaba da yi mini addu'a, jikina ne babu daɗi" Al'amin bai matsa da bincike ba, ya ƙyale shi. Jauhar ta yi mamaki da ya kawo mata atamfa, sai Nura ne ya turo da kuɗi a saya mata iri ɗaya da mamansa. A lokacin ta ƙara yadda da ƙani ya ɗauki Nura, da wani ne daban ya bata, cewa zai yi ba zata saka ba. Al'amin da kansa tare da rakiyar su Walid, suka je suka kaiwa mahaifiyar Nura, abun da ya aiko a bata, ta din ga murna tana yi wa Al'amin godiya tare da yi masa addu'ar gamawa da duniya lafiya. Mai unguwa kuwa raina dubu ashirin ɗin nan yayi, a ganinsa tun da Nura ya tafi Abuja, dubunan ɗaruruwa zai aiko masa, ya fara zargin ko Al'amin ne ya rage kuɗin. Ɓangaren Abbu kuwa, Abba ɗan wurin rahila, ya haɗa kai da abokai, suka fara yi wa Abbu sata, da ƙaramar sata suke yi masa, wani ya gani ya kawar da kai, wani kuma ma bai san sun yi ba. Sai dai a wannan karon, satar da suka yi masa ba ƙarama bace ba, dan har ya kai ga reporting wurin Jami'an tsaro, da fari rahila ta ɗauka abun mai sauƙi ne, dan ta na ta yi wa Abbu masifar a kan me zai tayi mata terere da ɗa dan ya ɗauki kuɗi, ai shi mai rufa masa asiri ne yayi masa nasiha, sai dai ta girgiza da ta ji ya saka 'yan sanda sun kama shi. Tamkar za ta yi hauka, da ƙyar ya saka aka sake shi, ya ce sai dai ya bar masa gida ya koma gidan ubansa, nan ma ta ce sai dai ya zaɓa ko dai ya zauna da ita da yaranta ko kuma idan ya matsa su tafi gaba ɗaya, ya ce ta kwashe yaranta su tafi. Sai da ta ga ba ta da sauran mafita, sannan ta koma lallaɓa shi, da ƙyar ya saukko. Juahar tuni ta fara zuwa awo, dan yau shi ya rakata awon ma, a wurin scanning aka nuna masa yadda zuciyar jaririn take bugawa. Gaba ɗaya ya rikice, bakinsa ya ƙi rufuwa, ya zubawa screen ɗin ido, yana ta washe baki yana murmushin. Jauhar ta ce "Ni fa na gaji zan tashi" Ya ce "Ɗan yi haƙuri, bari na ƙara ganinsa mana" "Ka ga me? Me ake ganewa a nan, ni banda duhu ba na ganin komai" Al'amin ya kalleta ya ce "Sautin bugun zuciyar ta sa ne nake ji har cikin raina" Sai da mai scanning ɗin ya yi dariya, aikuwa ta tashi zaune ta ce "Ni na gaji, haka kurum, na fuskantar tun yanzu kafi son ɗan tayin nan, to ka matso ka saukko da ni" Ya miƙe ya saukko da ita daga kan gadon, ya ce "Ki din ga motsawa a hankali, kar ki takura shi". Tayi murmushi ta ce "Idan ban tafi da gudu ba, ka ce ba ni ba ce" Ya ce "Yi haƙuri, ai dole na lallaɓaki" suka je aka gama yi mata awo, suka tafi wani shago na kayan jarirai, suka fara sayayya, kasancewar an ce musu tun a wata shida, kan ciki yayi bakwai ake haɗa kayan haihuwa, saboda haihuwa za ta iya zuwar mata a wata bakwai, sannan ya tanadi kuɗi, dan ba a san ya haihuwar zata zo ba, ko ta haihu da kanta, ko kuma ayi mata tiyata. Ta zo ta shirya kayan da suka sayo a wani ɓangare na wardrobe ɗin ta, kallon kayan kawai nishaɗi yake sakata. Washegari da safe, yana falo yana kallon wrestling, ta fito daga ita sai wata rigarsa da ta saka shirt ce, tayi mata yawa nesa ba kusa ba, iya cinyarta ta tsaya, sai kanta tayi kalba guda biyar, ta sake su ta fito tana miƙa tare da hamma. Ya buɗe mata hannayen sa, yana murmushi, ta ƙarasa ta zauna a kan cinyarsa, ya rungumeta ya ce "Sannu" "Yauwwa. Ina kwana?" "Lafiya ƙalau, ya jiki ya babyna?" Yayi maganar yana shafa bayanta. Ta ce "Ni babyn ko wa?" "Ƙatuwa da ke ke ce babyn, unborn dai" Boti ya hawo saman kujera, ya hawo jikin Jauhar, Al'amin ya kai hannu zai cillar da shi, ta riƙe shi tana dariya ta ce "Master dan Allah ka bari magen nan ya huta, duk ya tsaneka saboda cin zalinsa da ka ke yi, akwai buƙatar na yi muku sulhu" "Babu sulhu tsakanina da wannan abun" Ta ɗauki boti tana shafawa ta ce "Boti ku daina faɗa da master dan Allah" muzurun ya kawar da kansa gefe, Al'amin ya ƙwace shi ya ajiye shi a ƙasa, ya koma da baya yana kartar carfet ɗin yana yi masa kuka. Jauhar ta din ga dariya, ta ce "Wallahi daga kai har shi dariya ku ke bani" Al'amin ya lumshe ido ya buɗe, yana shafa cikinta ya ce "Duk kin zama ƙazama, kalli kin daina kitso, ga wata uwar riga kin saka, wadda sai an saka irinki goma a ciki, ni ɗaga rigar na din ga kallon jaririna" "Master kenan, ba zaka gane ba, ni kaina ba na son zama da kan nan a haka, amma da an fara yi mini kitso zafi yake yi mini, kayana kuma duk sun yi mini kaɗan, amma idan na saka rigar nan taka, balance nake yi a ciki" Ya kashingiɗa a jikin kujera, yana cigaba da kallonta, yana jin wani irin kusanci da shauƙin kasancewar sa da ita wuri ɗaya. Kullum yana ƙara girmama lamarin Ubangiji yadda ya ƙaddara kasancewar su tare, wanda idan ba ƙarfin ikon Allah ba, babu abun da zai haɗa shi da ita, har ya nemi aurenta. To wa ma zai bashi auren yarinya irin jauhar a yadda yake. "Master ka san menene?" Ya girgiza mata kai. "Na ji an ce akwai lokacin da ma'aurata kan gaji da juna, ko miji ya ji matarsa ta gundure shi, dan Allah idan Allah ya raya mu ka fara jin irin haka a kaina, dan Allah ka yi haƙuri kar ka canza mini, na saba da kai sosai da sosai. Ina jin daɗin yadda na samu mai tausayina wanda ya mayar da ni mutum, yake zama ya saurari damuwata. Dan Allah ko nan gaba ka samu wadda ta fini, ko na fara gundurarka kar ka yi mini wulaƙanci ko ka manta da ni dan Allah" tayi maganar very serious. Ya ƙura mata ido, yana mamakin maganganunta. "To ai ni ko yanzu kin gundureni, duk kin hana ni rashin ji na, na saba da rayuwata ta ɓalla ƙarafa da hawa network duk kin hanani, zaman haƙuri kawai nake yi da ke, kin isheni" Wasa yake yi mata, kawai ya ga tana kuka. A ɗan rikice ya ce "Haba Madarata, ke yanzu idan aka ce miki zan yi miki abu makamancin haka zaki yadda? Ina sake maimaita miki ni ɗan halak ne bana manta alkhairi. A lokacin da kowa ya yasar da ni, yake yi mini kallon mara amfani a lokacin ki ka rungumeni a yadda nake, ki ka yi ya ɗawainiya da ni, ba tare da kin gaza kin ƙosa ba, bana fatan Allah ya nuna mini ranar da zance kin gundureni" Ta share hawayenta ta ce "Ka san wani abu, kai diamond ne da mutane ba su farga da shi ba, suke maka kallon mara amfani. Sai yanzu da ƙyallinka da haskenka ya fito" Ya kwantar da kanta a ƙirjinsa yana murmushi ya ce "Ke dai ki ke kallon hakan, ga al'umma na zama mara amfani, saboda ɗan daba ne ni" "To ni dai kana da amfani a wurina" Yayi murmushi ya ce "A ɓoye fa rigima kawai ki ke so ki yi na rarrasheki, to na ji sannu yi haƙuri" "Yauwwa mata da yawa ba ayi mus irin yadda ka ke yi mini ɗin nan, zuciyar zinare ce da kai master, kana da tausayi sosai da sosai" ta kara kunnenta a ƙirjinsa ta ce "Zuciyarka sai kiran sunana take" Al'amin ya ce "Ni dai yi magana a hankali, na ji babyna yana motsi, kar kwanciyar da ki ka yi ce kika takura masa, tashi zaune" Ta ɗaga kai ta kalleshi ta ce "Master, zaka dawo ka tarar da ni, ina 'yar gala-gala da cikin nan, duk sai nuna banbanci ka ke yi" Shi ma kallon fararen idanunta yake yi yana dariya, ya ce "To breakfast fa, me zamu ci?" Ta tashi zaune ta ce "zan dafa maka wani abun, amma ni anty wasila nake jira, za ta kawo mini wainar gero" Ya tsuke fuska ya ce "Roƙo ko?" Ta ce "A'a geron da ka kawo na ɗiba na bata tayi mini, idan ni na yi ba zan iya ci ba" Ya ce "Ok" Har azahar yana gida, jauhar ta hana shi fita, sai azahar yayi shiri ya fita, saboda sallar azahar, yanzu jauhar ta daina fama da shi a kan yin salla a kan lokaci. Sai ga anty lubabatu, ta zo maƙwabciyar su mai ba ta aikin bead a gida. "Oyoyo anty lubabatu, yau ke ce a gidan". "Yau gani na lallaɓo, an ce mini kin kusa juyewa, na ce bari na zo ga ya kike" Jauhar ta ce "Ohh ni zahra'au in ji wa? Ba a gaya miki daidai ba" "Eh ba a gaya mini ba, ni na gani yanzu ai" Da sauri jauhar ta kalli cikinta ta ce "Haba dai dan Allah a na gani" Anty lubabatu ta kwashe da dariya ta ce "Lallai yarinya, wannan uwar ƙibar da ki ka yi ma da haka ki ke? Kin zama uwar mata" Juahar ta yamutsa fuska ta ce "Na yi muni ko?" "A'a babu wani muni, wallahi kin yi kyau, kallo ɗaya mutum zai yi miki ya san a kwanciyar hankali ki ke. Jauhar gyaran gida aka yi miki haka, lokacin da na zo gidan nan kina amarya tsurar bulo ne fa, ikon Allah har da sola, wato a duniya idan Allah yana yinka ko wa ma yaƙi ka. Ga Alhaji mu'azzam can Allah ya bar su da shi, matarsa na ta gana wa hafsa azaba, abu har da 'yan sanda, ya ce idan ba zata zauna da matarsa lafiya ba tayi mata biyayya ta tafi gida. Gidanku kuma ana ta tashin hankali, Anty zakiyya ta ce mama ke yi mata asiri" Cikin damuwa jauhar ta girgiza kai ta ce "Bari kawai Anty lubabatu, lamarin gidan nan namu sai Innalillahi wa Innalillahi raji'un, kuma wasu lokutan har da laifin baba, kodayeke shi ma sun mayar da shi sai yadda suka yi da shi, ai da ni aka ce ina yi wa hafsan asiri. Ko gidan ya hanani zuwa, sai idan da daddare ya kaini na gaida baba na dawo gida" "Allah ya taimake ki, ke da suka so su tozarta rayuwarki Allah ya rufa miki asiri, ɗan daban da suka aura miki dan ki wulaƙanta, hakan ba ta faru ba" "Tababs babu abun da zan ce wa Allah sai godiya, Anty lubabatu mijina a maza ɗari irnsa ɗaya ne tak. Daba da shaye-shaye su ne ƙaddararsa amma, ya ci sunansa amintacce rauninsa mutane suke kallo, basa kallon nagartarsa" sun daɗe suna hira sosai kafin ta tafi. Kusan duk bayan kwana biyu zuwa uku, sai hajiya kakar Al'amin ta kira Jauhar ta yi mata ya jiki, dan tun wani zuwa da tayi ta fuskanci hakan. Tun da ya fita da azahar har bayan magariba bai dawo ba, sai da ta kira shi a waya, ya ce mata gashi nan. Hnakali a tashe ya dawo mata, dan sai da gabanta ya faɗi ya ce "Master lafiya?" "Nura aka kawo daga Abuja, wai ba shi da lafiya, tun lokacin nan da ya ce mini ba shi da lafiya, yake kwance" Ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, meya same shi haka?" Ya ce "Ban sani ba, an dai kai shi asibiti, na je na ganshi a galabaice, yayi magana ya faɗi meyake damunsa ya ƙi, na ga a galabaice yake sosai, an saka masa ruwa da sauran abun da yakamata gobe in Allah ya kaimu dai zan koma". Jiki a sanyaye ta ce "Allah sarki Nura, sai da ka ce idan ba zai iya ba ya dawo, wataƙila dan kar ka yi masa faɗa ne ya zauna bai dawo ba. Allah ya bashi lafiya" Ya amsa da Amin. Ya ciro mata envelope ya ajiye mata. Ta ce "Menene wannan?" Ya ce "Duba ki gani mana" Hotunasu ne shi da ita, wanda galibi a wayarta suka yi, ya kai aka ciro su, sai kuma ƙatuwar viva, da aka yi frame ɗin hoton da suka yi na sallar eid ɗaya an rubuta musu happy marriage life, ɗaya kuma an rubuta first eid with habibi. Tayi murmushi ta ce "Kamat yayi a rubuta Master weds madara" duk da a cikin damuwa yake sai da yayi murmushi, ya ce da safe zai kafe a falo. Ta kalleshi tana murmushi, bai taɓa ce mata yana son ta ba, sai dai actions ɗin sa, yana tabattar mata da hakan. Da fari kai ba ka ce ya iya duk wani abu da yake da alaƙa da kulawa ba, saboda he's always serious, sai dai a hankali ainihin halayensa suke fitowa. Jikin Nura yayi tsananta, kullum Al'amin cikin sintiri yake, jauhar ce mai lallaɓawa tayi musu girki, mahaifiyarsa ce take zaune da shi a asibiti tana kula da shi, gashi an rasa gane abun da yake damunsa, Al'amin har gona ya saka aka sayar masa a ƙauye, saboda kula da Nura, dan asibitin kuɗi ya saka aka mayar da shi. Da daddare babar Nura ta fita, Al'amin ya zo, cikin ƙarfin hali ya ce wa Al'amin "Yau ina Antyna ba ta zo ba?" Ya ce "Eh, ni na hanata zuwa, tayi nauyi. Nura yakamata zuwa yanzu ka gaya mini menene yake damunka, ana ta kashe kuɗi an rasa gane abun da yake damunkaa yayi maganar cikin damuwa" Nura ya ce "Idan na gaya maka ba zaka yi fushi da ni ba?" "Ya za ayi na yi fushi da kai? Ka gaya mini in san ta in da zan kamo bakin zaren". Ya riƙe hannun Al'amin ya ce "Na san ba lallai na rayu, amma ba ka da laifi ka taimaki rayuwata ne. Na gayawa mama na ce kar ta gaya maka. Lokacin da na ce maka na fasa tafiyar nan, Honorable ne ya ce sai ya yi ɗabi'ar mutanen annabi luɗ da ni, na ƙi yarda, ni kuma na kasa gaya maka, dan ya ce idan na gaya maka, kashe mai unguwa zai yi, amma idan na amince shikenan, ba wanda zai san an yi kuma zai bani aikin. Na ɗauka daga haka shikenan, sai dai tun da ya tafi da mu, a wani gida aka ajiye mu, abun da suke yi mana kenan, yana da masu kula da mu, babu ta in da mutum zai gudu, kuma ba shikaɗai ne yake yi mana hakan ba, akwai wasu manyan mutane a ƙasar nan, da duk zan gaya maka sunayensu. Kuma kamar tsafi suke yi ta hanyar amfani da mu, bana iya riƙe bayan gida, mama ce take gyara mini kafin mutane su zo dubiya, Indabo ya lalata mini rayuwa amma ka rufa mini asiri dan Allah, kuma kar ka zargi kanka! Ina da hujja mai ƙarfi da zan baka a kan haka! Ayshercool. 08081012143 45 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Gaba ɗaya fuskar Al'amin ta sauya takmar ta horo, ta koma Al'amin ɗin sa na ainihi, tamkar bai taɓa sanin wani abu wai shi dariya ba. Wani irin gumi ya shiga tsatstsafo masa, jijiyoyin goshinsa zuwa kansa suka miƙe suka kukkumbura, idonsa yayi wani irin ja mai ban tsoro, bugun zuciyarsa ya ƙaru da saurin gaske, jikinsa ya fara ɗaukar wani irin zafi saboda tashin hankali da tsananin ɓacin rai. Ba tare da tunanin halin da Nura yake ciki ba, yayi wa hannun guduma wani irin mugun riƙo, da sai da ƙasusuwansa suka yi ƙara. Nura ya ɗora ɗaya hannun a kan na Al'amin ya ce "Yaya, kai ɗan uwa ne da Allah ya bani rana tsaka a titi, duk wannan abun ka yi ne dan inganta rayuwata, ba ka taɓa yin wani abu da zaka cuceni ba, na san da ka san abun da zai faru da ni kenan, ba zaka bari na je ba, dan Allah ka kwantar da hankalinka, ni na san ba zan rayu ba, abun da suka yi mini ya fi na kowa muni da tashin hankali, ban san yaya zan misalta maka ba, amma dan Allah kar ka yi yinƙurin yin wani abu, idan ba haka ba za su yi maka illa. Na bar su da Allah ka tayani Addu'a Allah ya yafe mini laifukana, idan na mutu dan Allah ka yi mini wanka kar asiri na ya tonu, ba na son a zargeka da abun da mutane ba su san menene ainihin abun da ya faru ba. Wurin bayan gidana ya riga ya ɓaci, kowa ya gani zai gane meyafaru dan Allah kar wani ya je kan gawata idan ba kai ko mama ba" Al'amin ya riƙe hannun Nura gam, amma ya kasa magana sai wani irin numfashi mai haɗe da huci, ya sunkuyar da kai yana sauke numfashi. Yanayin yadda mahaifiyar Nura ta tarar da Al'amin, ya sanya ta gane ya gaya masa. Ta ƙarasa gaban gadon, jiki a sanyaye ta ce "Al'amin, ka kwantar da hankalinka dan Allah, zan iya dafa Alqur'ani na rantse, ba zaka kai mini nura in da za a cutar da shi ba, na san da ka san me zai faru kenan ba zaka yadda ya je ba, a irin yadda yake bani labarin zamanka da shi. Iya ɗawainiyar da ku ka din ga yi da mu kai da matarka ya ƙara tabattar mini da haka. Cuta ce an riga an cuce mu, amma mun bar wa Allah, ni ba zan zargeka ba" Ya saki hannun Nura a hankali, ya tashi ya juya ya fice. Nura yayi ajiyar zuciya ya ce "Allah ya sa kar ya ce zai ɗauki wani mataki, dan mutanen nan sun wuce duk yadda yake tunani, ni dai ku cigaba da yi mini addu'a da fatan cikawa da imani" Duk da juriya da mahaifiyar Nura take yi, sai da ta kasa ta zubar da hawaye, cike da karaya, dan magana kawai Nura yake yi, amma komai sai an yi masa, gashi buni-buni jininsa ya ƙone, sai an saka masa wani, dan bayan bayan gidan, har da jini ne yake zuba daga wurin, jini sosai ba kaɗan ba, a tunaninsa da na mahaifiyarsa ɓoye wa likitocin ainihin abun da ya faru shi ne rufin asirin su, dan babu wanda zai fahimce su, cewa za a yi shi ya kai kansa, saboda kwaɗayi da son abun duniya, dan Nura ya yi girman da ya fi ƙarfin ace dole aka yi masa. Ikon Allah ne kawai ya kai Al'amin gida, dan ko me za ayi masa bai san ya aka yi ya isa gidan ba. Jauhar har ta yi bacci, dan 'yan kwanakin nan bacci take yi sosai da sosai, duk in da ta ji kwanciya ta yi mata daɗi sai bacci. Ba ta farka ba, sai bayan sha biyun dare, shi ma dan taji ta gaji da kwanciyar ne, a hankali ta tashi jikinta duk yayi tsami, ta kalli ƙofar ɗakin Al'amin, ta tashi ta nufi ɗakin, ta ɗaga labule ta shiga. Yanayin kwanciyar da ya yi, ya tabattar mata da yayi shaye-shaye ya bugu, dan wata irin kwanciya yayi. Jiki a sanyaye ta ƙarasa gaban katifarsa ta zauna a hankali ta ce "Haba master yau kuma?" Dan bai fiye shan abun da zai gusar masa da hankali gaba ɗaya har haka ba, yana yi amma ba sosai ba, ya fi ganewa busa hayaƙi. Kuma kwanakin nan da Allah ya taimaketa tayi galaba a kansa, bai fiye shan abun buguwa ba sai shan sigari, wiwin ma ya rage shan ta sosai, amma ta zo ta tarar da shi a wannan yanayin. Da ƙyar tana haki, haka ta gyara masa ƙafarsa da hannunsa, ta shafi sumar kansa, sai wani irin gumi yake yi, naman fuskarsa yana ɗan yi rawa lokaci zuwa lokaci ga ajiyar zuciya da yake ta yi a kai kai. Ganin ba ya hayyacinsa, balle su yi magana, ya sanya ta tashi ta tafi ɗakinta, cikin zullumi da tunanin me aka yi masa?. Kiran sallar farko ya farka, sai dai zuciyarsa cike da tsananin baƙin ciki da ɓacin rai, ya san ko ya je gida ba zai samu indabo ba yana Abuja, kuma ba zai iya tafiya Abuja ba, cikin fargaba zai tafi kar yana matsawa wani abun ya samu Nura. Alwala yayi ya fice, a hanya yayi sallar asuba, ya ƙarasa Asibitin, maman nura na ta kokowar yadda zata ɗaga shi, ta saka masa pampers, yayi mata girma. Al'amin ya bubbuga ƙofar, ta ce "Waye?" Da ƙyar ya iya magana ya ce "Al'amin ne" Nura ya ce "Mama buɗe masa" Ta buɗe masa ya shigo, Nura ya gaida Al'amin, jinjina kai kawai yayi, suka gaisa da maman Nura, da ƙyar yake iya magana, saboda tsananin ɓacin rai da tashin hankali. Ya taimaka mata, suka canzawa Nura pampers, jinin da Al'amin ya gani a pampers ɗin ya ɗaga masa hankali, gaba ɗaya halittar duburar Nura ta fito waje, babu ƙyanƙyami babu komai, ya taimaka mata suka gyara shi, suka saka masa pampers uku, kamar yadda take saka masa, sai kuma ta kawo zannuwa ta tuttura masa ta toshe ko ina, ta fesa masa turare, ta kunna turaren wuta, ta shiga banɗaki ta wanke kayan da aka cire mas. Al'amin ya rasa me ma zai cewa Nura, abun duniya ya ishe shi, ya ji ya tsani kansa, komai baya yi masa daɗi. A hankali ya kalli Nura ya ce "Zan gaya wa likitoci, su duba idan da abun da za a iya yi, ayi maka babu dabara a ɓoyewa likitoci wannan lamarin" Da sauri Nura ya ce "Dan Allah kar ka yi mini haka, ka rufa mini asiri, wallahi babu wanda zai yadda dole aka yi mini, na san ba zan rayu ba, lokaci kawai nake jira, dan Allah yayana wannan ce alfarmar ƙarshe da zan nema a wurinka, dan Allah kar ka gaya wa kowa" Cikin matsananciyar damuwa Al'amin ya ce "Nura ka yafe mini, wallahi ban san abun da zai faru ba kenan, na zata hakan zai taimaki rayuwarka ne... Sai ya kasa ƙarasawa muryarsa ta fara rawa. Guduma ya ce "Wallahi na sani, kai mutumin kirki ne yayana, dan Allah idan na mutu ku din ga yi mini addu'a, na san sauran jama'ar gari babu lallai su yi mini, saboda ban shuka alheri ba, amma na san kai zaka yi mini kai da mama, da Antynmu. Dan Allah idan ta haihu, idan namiji ne, ka saka masa Nuraddenni ka din ga tunawa da ni" yayi maganar yana murmushi. Al'amin ya haɗiye wani abu mai tsananin ɗaci, ya kalli Nura, amma ya kasa magana. Nura ya sunkuyar da kai, yana share hawayen karaya. Maman Nura ta fito ta gama wanke kayan Nura, muryar sa na fita a hankali, ya kalli maman Nura ya ce "Me za a sayo muku ne? Da me zaku karya ba ta tashi ba na taho" Mama ta ce "Kar ka damu Al'amin, ƙanwata suna nan tafe, da wuri za su zo, ai da ƙannensa ma su duba shi, baiwar Allah ai tana ƙoƙari Allah dai ya raba ta da cikin nan lafiya, ta sauka lafiya ƙalau. Ai ta ce tuwon dawa zan yi mata, da miyar ɗanyar kuka da man shanu idan ta haihu, in sha Allah kuma ana ce mini ta sauka, zan dafo na taho kano, yajin daddawa ma ni zan yi mata". Nura ya ce "Mama ni dai ki tayani roƙo, na ce a saka sunana idan an samu ɗan saurayi" Suna yin hirar ne, dan Al'amin ya kwantar da hankalinsa, sai dai fuskar nan tamau ya kasa yin fara'ar. Ƙarfe takwas da mintuna, wata yarinya ta shigo ɗakin, 'yar baƙa mai kyau, da siririn billenta, a gefen fuskarta. Babu ko sallama ta faɗo ɗakin ta ce "Mama mun zo" "Baki iya sallama ba ne?" Ta ce "Assalamu alaikum, yaya wai da gaske ka je Abuja?" Tayi maganar tana ƙarasawa gaban gadonsa. Nura ya ce "Eh ramma, ya gida ya makaranta?" Ramma ta ce "Lafiya ƙalau, yaya wai to ka ga shugaban ƙasa?" Ya girgiza mata kai alamar a'a. "To idan ka koma zaka ganshi? Ka ce masa dan Allah a gina mana burtsatse, wurin ɗebo ruwa da nisa sosai" Ya shafa kanta ya ce "To zan gaya masa, ina Sani?" "Babanmu ya ce ba za a zo da shi ba, ya tafi makarantar Allo, nima da ƙyar ya bar na biyo innar su jafarun muka taho". Mama ta ce "Ke baki iya gaisuwa ba, balle ki yi wa yayan naki yaya jiki ba?" Ta kalli Al'amin ta durƙusa ƙasa ta ce "Ina wuni?" Ya jinjina mata kai kawai, ta ce "Yaya sannu ya jiki?" "Jiki da sauƙi Alhamdilillah" "To Allah ya baka lafiya" Wata mace ce tayi sallama, tana faɗin "Ke kuwa ramma an yi ƴar bantan uba, ina can ina bulayin in da aka kwantar da ku, kawai na nemeta na rasa shashasha ba zaki yi hankali ba" Ta zauna suka gaggaisa, Mama ta nuna mata Al'amin ta ce "Atine ga uban gidan Nura, shi ya samo masa aikin nan, yake ta ɗawainiya da mu" Atine ta ce "Allah sarki, ni wallahi kama yake yi mini da mai gyaɗa, yana kama da 'yar nan ta ta da ta rasu wadda tayi aure a birni, zahra'u" da sauri Al'amin ya kalleta Mama ta ce "Wallahi kuwa, mun yi waya da ita ma, ta ce zata zo duba Nura". Taɓ yana da alaƙa da Nura ne, ko kuwa kawai dai hasashe ne, ko abun su na mutanen ƙauye, da kowa ma ɗan uwan su ne? saboda tsabar miskilanci bai yi musu magana ba, ya tashi ya tafi. Ya je gidansa ma, ya kasa kawai ya tafi ya samu wani kango, yayi zamansa, abun duniya ya ishe shi, bai ma san ta ina zai fara ba. Bai koma gida ba sai can bayan la'asar sannan ya koma gida, ba ta ce masa uffan ba, tayi masa sannu da zuwa, ita babbar godiyarta ga Allah, dawowarsa lafiya, ba tare da wani abu ya faru da ita shi ba. Sai dai ta haɗa abinci ta bashi, amma ta ga ya daɗe bai motsa ba, daga baya ya ɗauki cokali ya din ga tura abincin da ƙyar, kamar mai tura magani, ya gama ya nemi wuri ya kwanta bai ce mata uffan ba. Duk da yanayin hakan bai yi mata daɗi ba sam, amma ta daure ta ɗan bashi lokaci, amma taga a jere, kusan kwana uku, ba ya ce mata uffan, kuma kullum sai ta yi bacci zai dawo, da asubar fari kuma yake ficewa. Idam ya fitan nan, asibiti yake tafiya ya taimakawa babar Nura ta gyara masa jikinsa, sai dai kullum jikin nasa babu sauƙi. Ranar na haɗu, da ya fito zai fita ta tare shi ta ce "Master, wai dan Allah laifin me na yi maka har haka ne? Meyake faruwa yakamata ka sanar da ni" Ya ce "Zan gaya miki idan na dawo" daga haka ya fice ya bar ta. Abun duniya ya ishi jauhar, ta kasa gane meyake faruwa haka yake ɓoye mata. Yana zuwa asibiti ya tarar da mahaifiyar Nura a gefen gadon Nura, ta rufe shi, idanunta sun yi jawur. Cikin matsanancin tashin hankali ya ƙarasa gaban gadon, ya yaye zanin, ya tarar Nura ya cika. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" ya furta cikin matsanancin tashin hankali, ya zauna yayi shiru shiru, ya kasa zubar da hawaye sai wani abu da yake yi masa zillo, tsakanin maƙogwaronsa da ƙirjinsa. Ya saka gwiwoyinsa a ƙasa a gaban mahaifiyar Nura ya ce "Ki yafe mini saboda girman Allah, ban taɓa tunanin abun da zai faru da Nura kenan ba, da na san haka zata kasance wallahi ba zan tura shi ba" Ta share hawayenta ta ce "Wallahi na sani, kuma ni ban zargeka ba, Yanzu fatana Allah ya sa mutuwa hutu ce a gare shi, Allah ya yafe masa kai ma ɗawainiyar da ka yi da mu, Allah ya baka lada". Ya ɗauki waya ya sanar da su liti su samo mota, a asubar su zo a tafi da gawar Nura Allah ya yi masa cikawa. Sun girgiza sun kaɗu matuƙa da mutuwar Nura, da asubar aka tafi da gawarsa gidan mai unguwa, ta ce ita za ta yi wa Nura wanka, Al'amin ya tayata ya ce ban da su biyu, kar wanda ya je kan gawarsa. Mai unguwa ya din ga bala'i, yana yayi asara kuwa, ya rasa wanda zai gayyato kan gawarsa sai ɗan daba. Maman Nura ta ce "Ɗa na bai yi asara ba wallahi, kai ka yi asara, dan da ka kula da shi ka riƙe shi da mutunci da amana, ba zai faɗi haka ba. Kuma ba in da aka ce ɗan daba ɗan wuta ne, ko an haramta masa zuwa kan gawa". Haka suka yi wa Nura sutura, aka sanar da rasuwar sa. Duk da ana ganin Nura baya ji, amma ya tara mutane, saboda daga baya duk wani aikin gayya na cigaban unguwa da shi ake yi. Sai ƙarfe goma na safe, Al'amin ya dawo gida, yana zullumin yadda zai gaya wa Jauhar mutuwar Nura, ga zuciyarsa da take wata irin tafasa take raya masa kashe Indabo ya huta da baƙin cikin da ya jefa shi a ciki. Cikin matsananciyar damuwa ta ce "Master wai meyake faruwa dan Allah?" "Allah ya yi wa Nura rasuwa" Gaba ɗaya sai ta manta waye ma Nura, ta ce "Waye kuma Nura?" Ya ce "Guduma ɗan gidan mai unguwa" kamar shashasha haka ta bishi da kallo, daga bisani wani irin jiri ya ɗebe ta, cikin azama ya riƙe ta, jikinta ya hau wata irin tsuma, ta saka hannu iya ƙarfin ta, ta toshe bakinta, dan hana kukan da yake ƙoƙarin taso mata fitowa amma ta kasa, iya ƙarfinta ta din ga maimaita "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Allah ya sa ba Nuran da na sani ka ke faɗa ba" Jiki a sanyaye ya zauna da ita a jikinsa ya ce "Ba kyau yi wa mamaci kuka fa kin sani, ki yi masa addu'a" Cikin kiɗimewa ta ce "To me zan ce?" "Ki ce Allah ya jiƙan Nura yayi masa rahama" Tari ta fara yi, ya ɗaga ta yana yi mata fifita, tare da yi mata sannu. Sai da ya tabbatar ta ɗan samu nutsuwa, sannan ya riƙe hannunta, suka tafi gidan mai unguwa, idanunta sun kumbura sun yi jawur, fuskarta ma tayi ja sosai da sosai. Sai dai suna shiga ɗakin da mahaifiyar Nura take karɓar gaisuwa, suka tarar da hajiya a ciki a zaune, a kusa da Maman Nura. Hajiya ta ce "Al'amin, yanzu nake cewa zan kiraka na ga kamar unguwarku ce nan" Maman Nura ta ce "Ai wannan ne ubn gidan nasa da ya ɗauke shi kamar ɗan uwa da nake gaya miki" "To ai ɗan wurin Zahra'u ne, jikana ne" "Iko sai Allah, Al'amin da kakarka da mahaifiyata uwar su ɗaya uban su ɗaya, Allah bai saka mun san juna ba" Ya zaunar da jauhar, ta zubawa mahaifiyar Nura ido, amma ta kasa magana sai sheshsheƙar kuka, maman Nura ta rungumeta tana ƙoƙarin rarrashinta, amma ta kasa sai suka cigaba da kukan tare gefe ga ramma da ƙaninta sani, da suke uwa ɗaya da Nura, suma su na ta kuka, hakan ya ƙara karya zuciyar Al'amin. Har aka gama zaman makoki, Al'amin yana cikin damuwa da tashin hankali, Hajiya da su ramma, a gidan Al'amin suke kwana, har zuwa kwana bakwai, sai dai kafin a gama zaman makoki, mai unguwa ya fara yada maganganu cewar Al'amin ne yayi silar mutuwar ɗan sa, Allah kaɗai ya san ina ya kai shi, idan abun gaskiya ne, meyasa shi bai je ba ya tura shi. Kafin a ƙare zaman makokin, sai da maman Nura suka yi kaca-kaca da mai unguwa, ta ce Al'amin babu yadda za ayi ya kai shi in da za a cuce shi, idan ma haka ne, ai ɗan uwansa ne ba ruwansa. Aka share zaman makoki, amma Al'amin ya kasa cigaba da walwala, tun jauhar na bin sa na tambayarsa ko lafiya? Ta yi rarrashin tayi ban bakin, har ta gaji ta zubawa sarautar Allah ido. Zuciyar sa na ta azalzalarsa ya bi Indabo can Abujan, ya halaka shi kowa ma ya huta, amma ya daure ya jira ya dawo. Sai da Nura yayi sati uku, sannan aka gaya wa Al'amin Indabo ya dawo. Gaba ɗaya baya cin abinci yadda yakamata, idan ya fita baya iya zuwa wurin sayar da shayi, sai ya samu wurin da babu wanda zai takura masa ya kwanta yayi ta tunani, ya din ga jin da ma bai san Nura ba a rayuwarsa gaba ɗaya da duk haka bata faru da shi ba, ashe duk abun nan ma suna da alaƙa da juna. Hatta jauhar yanzu ba ta iya samun kulawarsa yadda yakamata, dan ko in da take ya daina zuwa, ba ya dawo wa ma sai ta yi bacci. Gashi ta shiga wata na bakwai, haki ya sakata a gaba, ga nauyin cikin ya fara damunta, da ƙyar take iya tafiya. Indabo yana zaune a falonsa, yana ganin mutane, ya ga Al'amin ya faɗo falon kamar daga sama. Cikin sauri ya sallami waɗanda suke tare da shi, ya miƙe tsaye ya ce "Mai zamani lafiya kuwa? Ya na ganka a haka?" Kafaɗar Indabo ya daka ya hantsila kan kujera, "Me zamani distinguish senator kamar ni ka yi wa haka, dan na sakar maka na ba dama a kaina?" "Zuwa na yi na gaya maka shukar da kayi tayi huda". "Kamar yaya?" Al'amin ya kalle shi da jajayen idanunsa ya ce "Ba na jin magana, amma wallahi ba na cin amana, kuma duk wanda ya ci tawa sai ya biya. Nura guduma ya mutu, na karɓi saƙonka ka jira amsar da za ta biyo baya". Ras! Gaban indabo ya faɗi, dan ba haka suka tsara ba, ya aka yi ya san Nura ya mutu?. "Ban gane Nura ya mutu ba" "Shut up! Ka sam komai, tsohon munafuki algungumi, na san komai, ka lalata rayuwar yaron da nayi niyyar ingantawa. An dawo da shi rai a hannun Allah, na san baka san ya aka yi aka dawo da shi gida ba, bayan ka shirya yayi hatsari idan ya tashi dawowa yadda zaka ɓatar da abun da ka aikata. Wallahi ka ci amanar Al'amin kuma sai ka biya. Ba ka yi mamakin yadda nake yi maka biyayya ba na yi duk abun da ka ke so?, ka zata kawai saboda kana bani kuɗi ne? Bari na tuna maka ni yaron dodo ne, dodo babban sarki doodn da yake ɗauke da makamin tarwatsaka, ka zata ya mutu da sirrin nan a cikin sa ne? Wallahi ma'aruf na sanka fiye da yadda ka san kanka, a Nigeria ko wajen Nigeria wuraren da ka ke tafka tsiyatakunka. Wallahi na buɗe bakina a kanka, ka gama kaɗewa bar ganin kana da rigar kariya, kuma ku ne ku ke juyar ƙasar, dodo ya mutu ya bar ni da babban kundun da zan iya rusa ku. Niyyata idan na zo na kashe ka, sai dai hakan ba zai saka na huce ba, saboda yanzu ba irin da ba ne, na ajiye wanda suke buƙata ta. Akwai dabarun da masu kimiyyar lissafi suke bi, wurin yin solving wato BODMAS. Bracket Open, division, multiplication addition sannan subtraction. To ni upside down nake yi indabo, sai na fara division nake multiplication na yamutsa komai sannan na saka a bracket na rufe. Ka rubuta ka ajiye daga yanzu, ni ne babbar barazanar rayuwarka Daga yanzu duk motsin da zaka yi, zaka yi shi a tsakanin tarkunan da zan saka maka, ka daina shan ruwa cikin kwanciyar hankali, ni ne magajin dodo kuma zaka biya cin amanar da ka yi mini" ya juya ya fita yana huci. Cikin tsananin tashin hankali, Indabo ya tashi, ya ɗauki wayarsa ya daddana, ya kara a kunnensa. Cikin tashin hankali ya ce "Ya aka yi Nura guduma ya bar gidan nan, garin yaya? Waye ya dawo da shi kano ban sani ba wane munafukin ne ya rusa mana plan?" Jifa yayi da wayar, ya hau safa da marwa, cikin tashin hankali "Kenan kallon biri yake yi mini duk tsawon lokacin da muka yi tare? Amma Allah ya tsinkewa dodo albarka, ya ƙara tsine masa cin amanar da ya yi mana kenan?" Ya kuma ɗaukko wata wayar ya kira P.A ya ce "Maza ka ƙaraso gida ina nemanka". Ya ajiye wayar ya cigaba da kaiwa yana komowa. Afujajan P.A ya ƙaraso, ya ce "Yallaɓai ya ake ciki ne, meyafaru na ganka cikin tashin hankali?" "Dodo" P.A ya ce "Me dodon yayi?" "Dodo ya daɗe da kashe mu, kafin mu kawar da shi ashe ya gaya wa mai zamani komai? An dawo da yaron nan Nura kano, ya san komai, na yi waya wai an nemi obi an rasa, ya gudu yanzu ya san komai, na kaɗe idan yayi magana ya gama rusa ni, Allah ya tsinewa dodo albarka" "Ka kwantar da hankalinka, honorable wai waye wani mai zamani, me aka yi aka yi shi ne? Mutum nawa ka kawar kan mu zo in da muke yanzu? Ba zai tayar mana da tarzoma ba, bayan mun yi nasara kawar da shi kawai zamu yi" Indabo ya ce "Tayaya wannan yaron mai shegen taurin rai, da ƙarfin tsiya, ashe tsawon lokacin nan kallona kawai yake yi" P.A ya ce "Kwantar da hankalinka akwai abun yi, zan yi maka bayani". Cikin dare jauhar na zaune tana lazumi, tayi sallar dare, ta ji shigowar Al'amin, ta ɗan jira wasu mintuna, sannan ta bi shi ɗakinsa. Ƙwayoyi ta tarar da shi ya haɗa zai sha, cikin azama, ta durƙusa ta kwashe ƙwayoyin, ta dube shi ta ce "Akwai abun da ka ke ɓoye mini master, ba iya mutuwar Nura ce take damunka ba, akwai wani abu a ƙasa ka gaya mini. Baka saba ta'amalli da ƙwayoyi haka ba". Yayi shiru bai ce komai ba. "Master ka yi mini magana dan Allah ka gaya mini " tayi maganar cikin matuƙar rauni. "Ki yi haƙuri ki je ki kwanta, dare yayi" "Ka san kwana nawa nayi bana iya bacci, saboda damuwar da ka ke ciki? Kallonka kawai nake yi kar na takura maka ina jiran ka yi mini bayanin menene amma shiru, haba master ka gaya mini dan Allah" Ya juyo ya riƙe hannun jauhar, yana murzawa cikin matsananciyar damuwa, ya sunkuyar da kai ya ce "Duk da abun a ɓoye ne, amma bai kamata na ɓoye miki ba, bai kamata na bar abun a raina nikaɗai ba". Sai a lokacin ya gaya wa jauhar abun da ya faru. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" tayi ta maimaitawa cikin matsanancin tashin hankali. "Master, ka ga irinta ko? Yana ɗaya daga abun da ya sa nake ta fatan ka nesanta kanka da mutumin nan, ya cucemu amma kansa ya yi wa. Baka yi da niyya ba, Allah ya jiƙan Nura ya saka masa" Al'amin ya kifa kansa a kan cinyar jauhar, sai a lokacin ya ji wasu irin hawaye suka zubo masa. "Sadik ya mutu a sanadina, Nura yayi wulaƙantacciyar mutuwa a dalilina, na zama annoba kenan? Mahaifiyar Nura har ta mutu ba zata manta, ni na kai yaron ta, in da ka yi dalilin gurɓata masa rayuwa ba" Jauhar ta girgiza kai ta ce "Dan Allah ka daina faɗar haka master, kowa abun da Allah ya rubuta masa yake riska ba kaine sila ba" tana kuka tana rarrashin sa. Tun da Allah Nura ya mutu, Al'amin ya ƙara nutsuwa, babu abun da yake yi masa daɗi. Ita kanta jauhar ta kasa daina jin ɗacin rashin Nura, dan tun da Al'amin ya ce masa an samo masa aiki a Abuja yake murna, yake bata labarin shi wata yarinya ya gani yake so, kullum sai ya je ƙofar makarantar islamiyyar su idan an taso su ya ganta, yanzu yana fara aiki, idan ya ginawa mama gida a cikin kano, ta dawo sai ya nemi auren yarinyar, amma kar ta gaya wa master. Take yi masa dariya ta ce masa ai mamansa aure take yi sai dai ya haɗo da mijinta, ya ce ya fasa zai yi aure ya ɗaukko ramma ta dawo cikin gari, ta baro ƙauye. Ta ce "Ban da abunku Nura haryanzu fa da sauran ƙuruciyarka, ɗawainiyar aure da yawa fa". Ya ce "Ni dai kawai ki yi mini addu'a, da na dawo, zan fara zuwa wurin yarinyar nan zance" Da haka tayi ta tuna ire-iren hirarsu, da barkwancinsa, ta kasa mantawa da shi. Al'amin har tofa ya sake zuwa, ya yi wa mahaifiyar Nura gaisuwa, ya kai mata abun alkhairi, ya biya ya gaida Hajiya ya dawo gida. Jauhar cikinta yayi girma sosai, kamar kana fita ka dawo zaka tarar ta haihu, ƙafafuwan ta duk suka kukkumbura, saboda girman cikin, aka ce yana shiga wata tara ayi inducing ɗin ta ta haihu ta huta, dan bayan nauyin cikin kullum cikin haki take, a haka kuma take lallaɓawa ta je makaranta. Wurin shayin Al'amin kuwa, wasu irin kuɗi ne suke shiga suna fita, dan tun safe ake aikin ɗorawa da saukewa, ya zama chamber matasa sosai da sosai, duk da suna sayar da kayan shaye-shayen su a wurin, ba sa cutar Al'amin shi kuma ba ya yi musu mugunta. Da safe su yi shayi, da rana indomie shayi, taliya haka suke wuni saye da sayarwar abinci. Juahar sun gama haɗa kayan haihuwa, dan washegari ne ya kama ranar da za su je ayi mata inducing, tana ta jin tsoro yana kwantar mata da hankali. Ta ce "Master" Ya ce "Mmm" "Ka ji sai motsi yake yi, kamar ya san gobe in Allah ya kaimu za a fara inducing ɗin nan" Ya ce "Ya ƙagu ya ga daddynsa, Nuradeenin daddy, in sha Allah sunan Nura zan saka, kamar yadda na yi masa alƙawari". Ta ce "Allah ya jiƙan Yaya Nura ya sa ya huta" Ya ce "Amin". Cikin shagwaɓa ta ce "Amma a gabanka zan haihu master, tsoro nake ji, an ce haihuwa akwai wahala fa" "Ba wata wahala in sha Allah, ina kusa da ke, ina yi miki addu'a zaki haihu, Ni zai fara gani kafin ya ganki " yayi maganar yana sumbatar cikin nata. "Ni dai na fuskanci ba a so na, ta babynka kawai ka ke yi" tayi maganar cikin shagwaɓa. "Ni na isa? Dukkanku ina sonku madarata" "Ba wani, ni baka taɓa cewa kana so na ba". Yayi murmushi ya ce "Amma kina gani a aikace ai". "Baka taɓa faɗa ba" Yayi dariya ya ce "Ai ke da ruwan zinari aka rubuta sunanki a zuciyata. Ina sonki madarata, ina ƙaunarki ƙauna mai tsanani ya fi ubban shadidan" Ta ce "Wayyo Allah daɗi. Wallahi har cikin tsakiyar zuciyata na ji kalaman nan, ba ka taɓa gaya mini ba, ka cigaba da gaya mini, da daɗi" Ya ƙara rungumeta ya ce "I love you madarata" "I love you too babyna, kuma baban babyna, masterna abun ƙaunata" Har mamakin irin kalaman soyayyar da suka din ga musaya take yi, da ba ta taɓa tsammanin jin su daga bakin mastern ba. Cikin matsanancin shauƙin so da ƙauna, suka kasance cikin farin ciki. Suka yi wanka, ya rungumota daga toilet tana takawa a hankali da ƙaton cikinta a gaba. Ya taimaka mata, ta saka rigar bacci, sannan suka kwanta, ta kwanta a jikinsa, tayi balance da ta motsa sai yayi mata sannu. Wani irin nannauyan bacci ne yayi awon gaba da ita. Ji tayi kamar ana kokowa a falo, ta laluba ba ta ga Al'amin ba, ga wani irin ƙaurin taba ya cika ko ina. Hasken fitila ta hango an kunna ƙwan falo, ta saukko ta fito falon tayi arba da wasu matasa hannunsu riƙe da miyagun makamai, madaki ta fara ganewa gabanta ya faɗi. Sun rirriƙe Al'amin, suna shaƙa masa wani abu, jikinsa ya saki yana ta layi. Madaki ya bushe da dariya ya ce "Ka ce baka ji, dama ka ce da ni da kai sai wani ya kawo ƙarshen wani, to ni zan kawo naka ƙarshen yau ina dodon da kake taƙama da shi? Duk da zuwan ba nawa bane ba, na uban gidanka ne Indabo, amma ya jaddada mini in tabattar ka tafi da wani mugun miki a zuciyarka". Cikin tashin hankali jauhar ta janyo jikinta ta nufi in da Al'amin yake tana kiran sunan sa "Al'amin me ka yi musu ne? Dan Allah ku yi haƙuri mana". Al'amin ko harshensa ya kasa motsawa, balle wata gaɓa ta jikinsa. Madaki ya riƙo gashin jauhar, ya kalleta ya ce "Yanzu kin zama ragowa, ni kuma ba zan ɗana abun da yake ragowar maƙiyina ba, gashi kin zama cuus" ta riƙe ƙasan gashinta da Madaki ya riƙe. Cike da mugunta, ya saka ƙafa ya kawashe na jauhar ta gaba ya saketa, ta faɗi a kan cikinta, ta ƙwala wata irin razananiyar ƙara ta ce "Ya Allah, Ya Allah, Ya Allah" ta faɗa sau uku, take jini ya fara malala daga jikinta, harshen ta kawai take motsawa a hankali tana kiran sunan Allah, ta din ga ɗaga hannunta tana son kiran sunan Al'amin. Ya ƙura mata ido yana kallon ta, cikin buguwa da mutuwar jiki, tun tana ƙoƙarin magana a hankali har ta daina motsi. Madaki ya samu wani ƙarfe ya bugawa Al'amin a ka, shi ma suka sake shi a wurin. Ayshercool 08081012143. 46 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Wayar Walid ce ta fara ringing, yayi shiru ya cirota daga aljihunsa ya kara a kunnensa ya ce "Ya aka yi?" "Oga walid ka yi sauri ka dawo dan Allah, ya fara dawowa hayyacinsa, kar ya dawo gaba ɗaya ka san ba zan iya da shi ba". Walid ya ce "Gani nan, ka yi iya ƙoƙarinka, kar ka kuskura ya fita, idan ya fita akwai ƙura ka sani, gani nan zuwa" ya katse wayar ya sakata aljihunsa, ya kalli matasan ya ce "Ku mayar da ita kawai" ya juya zai tafi. Cikin azama Nabila da idanunta suka yi ja saboda kuka ta ce "Dan girman Allah ka yi haƙuri, kar ka tafi, ka ƙarasa mini labarin nan, yaya aka yi Viper ya tafi prsion? Shi aka ɗorawa kisan matarsa? Ta mutu ne ma ko kuwa yaya aka yi, ya kuma aka yi ya fito yanzu? Ni abubuwa da yawa ban gama fahimtar su ba, sun cukurkuɗe mini sun shige mini duhu, dan Allah kar ka tafi baka ƙarasa mini ba" Walid ya ce "Ba zan ƙarasa ba ɗin, ba dai ke mara mutunci ba, na ɗauka haɗuwarki da shi, zai zama alkhairi amma ki ka yi mana halinku na mata, laifina ne da na kawo masa ke, Al'amin ya daɗe da cire mata a rayuwarsa, sai zuwan jauhar cikin rayuwarsa daga kawo ki a tashin farko kin mayar mana da hannun agogo baya, Viper ba zai taɓa zama ya bar liti a tsare ba, saboda shi ɗan halak ne" Cikin matsananciyar damuwa ta ce "Na ji, na yi kuskure amma dan Allah ka yi haƙuri ka ƙarasa mini" "Ba zan ƙarasa ba, ki je shi ya ƙarasa miki" Cikin hanzari ta sake tarar Walid ta ce "Dan Allah ka sake yi mini jagora, ka kai ni wurinsa na nemi afuwarsa, na yi kuskure kaina ne ya riga ya gama kullewa na faɗawa lamuran a gaggauce cikin duhun kai, amma a shirye nake na gayara kuskuren da nayi" Walid ya ƙare mata kallo ya ce "Kin riga kin aikata abun da ba zai gyaru ba, kuma kar ki sake yin gangancin zuwa in da yake, idan ba haka ba, ko bai kashe ki ba ni zan kashe ki. Ku ɓatar da ita daga gabana". Suka saka Nabila a gaba, suka tasa ƙeyarta zuwa cikin napep ɗin da suka kawota, tana ta kallon walid tana yi masa magiya, amma suka ja babur ɗin suka tafi da ita. Suka mayar da ita hanyar law firm ɗin su, suka bata wayarta suka tafi, wani abun hawan ta tare, ta nufi gida, zuciyarta sai bugawa dake da sauri da sauri, cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali, ga matsanancin tausayin Al'amin da ya mamaye zuciyarta, lallai an yi wa rayuwarsa yankan ƙauna mafi munin da har ya mutu ba zai manta da shi ba. A falo magajiya take ce mata sumayya ta zo har gida tana nemanta, duk an kira layukanta ba sa shiga, ko akwai matsala ne, gashi yau ta daɗe sosai ba ta dawo ba. Ai har baba magajiya ta gama maganarta, ba ta fuskanci komai ba, ta tafi ɗakinta ta rufe ƙofa, wayarta na ta ringing ta duba, missed calls ɗin sumayya sun fi ashirin, ga na Nasir, ban da barrister Habib, ta kashe wayar, ta cillata kan gado, ta shiga banɗaki tayi alwala ta fito ta yi sallar azahar da la'asar. A kan daddumar ma haɗa kai da gwiwa ta yi, ta din ga kuka, za ta iya cewa tun da ta buɗe ido a duniya, ba ta ji labari mai ban tausayi da tsayawa a zuciya ba kamar na Al'amin. "Why Nabila kin yi garaje, why would you judge the book, according to cover? Why?" Ta tambayi kanta cikin tsananin takaicin abun da ta aikata. Ta kifa kanta a kan gadonta, wani abu tsananin ɗaci yana yi mata zafi a tsakanin ƙirjinta. Gaba ɗaya ta ji ta tsani kanta, wani mugun haushin kanta ya isheta. "Ko yaya yake ji a zuciyarsa yanzu? Dole ya zama bugagge gaba ɗaya, amma idan aka bar shi ya cigaba a haka, to tabbas zai haukace, amma yanzu yaya za ayi na samu ƙarashen labarin nan? Ta haihun ko mutuwa tayi, kuma wa ya kashe aka kai shi prison? Wait, to yaya ma aka yi aka sake shi daga prison ɗin, yana yawonsa idan ya ga dama har ya je yayi ɓarna, kuma still a haka wai nansa ake yi. Wai wannan wane irin lamari ne mai sarƙaƙiya haka? Kar na je na haukace a banza mana" tayi maganar kamar za ta haukace ɗin. Ta cigaba da sintiri, tana ƙirga yatsunta, tana lissafi. "Kai dole na samo ƙarashen labarin nan, ko da kuwa me zai yi mini, ko dai wanda ya fara ya ƙarasa mini, ko kuma shi Vipern ya ƙarasa mini, no matter how and what it takes sai na ji ƙarshen labarin nan, kuma sai na yi wani abu a kai. Haba dan Allah What a pitful life of his? Kai, to ita meye nata ma da za ayi mata haka? Me ta yi she don't deserve this at all" tayi maganar tana fashewa da kuka iya ƙarfinta. Bugun ƙofar ɗakinta ake yi, amma ko gezau, da ta gaji da jin bugun ma, sai ta tashi ta tafi banɗaki, ta rufe ƙofa ta kunna fanfo, ta cigaba da kuka da tunani. Ƙarfe takwas na dare Abba ya dawo gida, Nabila ya fara tambaya tana ina, Mama ta yamutsa baki ta ce "Ta dawo" Ya jinjina kai, ya tafi sashensa, har ya fara cin abincin dare, ya ajiye cokalin ya kalli mama ya ce "Kirawo mini ita, ina ga ba ta san na dawo ba" Haushi ya ƙule mama, ta tashi ta fita, ta je ɗakin Nabila, ta tarar da ƙofarta a rufe, ta din ga jijjiga ƙofar tana bugawa, amma ba ta buɗe ba. Magajiya ta ce "Hajiya tun da ta dawo fa ta rufe kanta a ɗaki, taƙi buɗe wa, ba yadda ban yi ba taƙi buɗewa" Mama ta yi tsaki, ta koma ta ce wa Abba, "To ka ji tun da ta dawo, ta rufe ƙofa taƙi buɗewa" "Kuma lafiyarta ƙalau?" "Ƙalau take, tsagwaron iskanci ne" Ya girgiza kai ya ce "No, ko an ɓata mata rai ne, a wurin aiki ko a gida, ƙyaleta na ganta da safe na ji menene, ko kuma rigimar ce ta motsa" yayi maganar yana murmushi. Wani malolon takaici, ya ƙule mama, yadda yake lallaɓa Nabila, yana bin ta kamar wata uwarsa. *** Abdul kuwa ganin ramma taƙi mayar da hankali ta ci abinci, hakan ba ƙaramin ƙular da shi yayi ba. Ita kuwa jikinta ne babu daɗi, ga kewar gidansu, tana tunanin mama, ga baƙin cikin abun da yake aikata mata, gashi ya sakata a gaba duk sai ta kasa cin abincin. Tana cikin zancen zuci, ta ji hannunsa a kan fusarta, ta tsorata ta ja da baya, ya tsuke fuska ya ce "Meye haka ne?" Ya buɗe idonta, ya ga she's still pale. "Solomon" ya ƙwalawa kukunsa kira. Solomon ya fito tare da cewa "Yes sir" "Kana da kayan miya ko?" Solomon ya jinjina kai alamar eh. "Kawo mini tumaturi manya guda uku, da wuƙa ka haɗo mini da Apple ja guda biyu" Ya ce "Ok sir" ya cigaba da kallon ramma, da ta ajiye cokalin, ta hau jan rigarsa da take jikinta, tana rufe ƙafafuwanta. Mintuna kaɗan solomon ya dawo, da plate biyu, ɗaya ɗauke da tumatir, ɗaya kuma Apple sai ƙaramar wuƙa guda ɗaya. Ya karɓa, ya matsa kusa da ita, ya ɗora ƙafarsa ɗaya a kan cinyoyinta, ta ɗago cikin rauni idanunta sun tara hawayen takaici, ya yanka tumatirin ya miƙo mata. Ta tsaya tana kallonsa tana kallon tumaturin. Miƙa mata yayi bakinta, ta kawar da kanta ta ce "Ni ba zan iya cin tumatur a haka ba" "Zaki karɓa ko sai na burma miki wuƙar nan a ciki?" Yayi mata maganar cikin tsawa. A tsorace ta buɗe baki, ya din ga bata tumaturin nan, tana taunawa da kyar. A zatonta zai bata tuffar, ta washe bakinta da ta ci tumatur, amma ya hau yanka tuffar yana ci, yana yi mata tauna a fuska, yana kallonta ga ƙafarsa a kan cinyoyinta da tayi musu nauyi. Ya gama cin Apple ɗin sa, ya taɓa wuyanta ya ji babu zazzaɓi, ya ce "Haryanzu kina zubar da jinin ne sosai?" Tayi masa banza kamar ba da ita yake ba, ya harzuƙa ya ɗaga hannu zai kwaɗa mata mari, ya ga ba ta motsa ba, sai hawaye da yake bin kuncinta. Ya janye ƙafarsa daga kan cinyarta, ya ce "Ki cigaba da ina yi miki magana kina kallona, ki yi mini banza kashe ki zan yi a banza" tayi shiru ba ta tanka masa ba. Jin ana knocking ɗin ƙofar falon, ya sanya ya tashi tsaye, ya ce "Tashi ki tafi ɗaki, za a shigo". Ga mamakinsa ko gezau ba ta yi ba, ta cigaba da zama tana zubar da hawaye. Zuba mata ido yayi, cike da tsananin mamakin shegen taurin kai a wurin kucakar 'yar ƙauyen yarinyar. Tashi tsaye yayi, ya fizgi hannunta, amma ta faɗi a wurin, saboda dama jikin babu ƙwari, ga jiri tana ta fama. Ya durƙusa ya ɗauke ta, ya nufi bedroom ɗin da ita, a bakin ƙofa ya dungurar da ita ta ciki, ya ja ƙofar ya rufe, ya koma ya buɗe ƙofar falon. Wata matashiyar budurwa ce a tsaye, sanye cikin doguwar rigar material, sai hula a kanta, hannunta riƙe da Jakarta. "Ko wata ce a ciki ne? Ina ta bugu amma baka buɗe ba?" Bai yi magana ba, ya bata hanya, ta shigo ta ajiye jakarta ta nemi wuri za ta zauna ta ce "Abdul, staining ɗin jini nake gani a kan kujerar nan" Cikin ko in kula ya ce "And so?" "Mace ka kawo gidan nan?" "Eh, akwai magana ne?" Cikin takaici ta ce "Abdul don't try me, ka sanni ka san halina, ba zai yiwu nayi dumping guys ɗina just because of you ba, and ka din ga rough play da ni ba" Yayi murmushi ya ce "Nina, ki na da matsala, saif ne ya yanke hannu da wuƙa, yana cin Apple, yayi bleeding sosai, amma ba abun da ki ke tunani bane ba" tayi ajiyar zuciya ta ce "Yauwwa ko kai fa, har hankalina ya tashi, i so much miss you" tayi maganar tana rungume shi. Gaba ɗaya sai ya ji banbarakwai, kamar ranar ya fara rungumeta, haka ya lallaɓata suka tafi ɗaya ɗakin sheƙe ayarsu, sai dai hankalinsa na kan ramma, kuma gaba ɗaya ya ji bai samu abun da ya samu a tattare da 'yar ƙaramar baƙauyyiyar yarinyar ba. Duk yadda ya so mazewa, sai sa Nina ta fuskanci hankalinsa a ba a kanta yake ba da tayi magana sai ya ce mata ba shi da lafiya ne. *** Har washegari, Nabila ba ta ci abinci ba, ta dai buɗe ƙofar cikin dare da zafi ya isheta, ta fara numfashi da ƙyar. Ta ɗaukko wayar Viper, ta din ga kallo, kamar shi ne a gabanta, ta rintse idanunta tana tuno kamanninsa, a zahiri suffarsa ta ban tsoro ce, amma a baɗini abun tausayi ne. Ƙarfe takwas na safe, yaran gidan na ta zuwa gaida Abba, sai da sauda ta shigo ta gaishe shi, ya ce "Sauda duba mini Arfa ko ta buɗe ƙofar, ki ce mata ina bata haƙuri idan laifi nayi mata, da ya sanya tun jiya ba ta neme ni ba, yau kuma ba ta zo ta gaishe ni ba" Sauda ta tashi, ranta a ɓace ta tsani yadda Abba yake sakata a shirgin Nabila ta girmeta gashi ba shiri suke yi ba, amma ayi ta zubar mata da girmanta. Ta je ta tura ƙofar ɗakin taga ta buɗe, taga Nabila a kwance a kan gado, ta kwanta a kan hannunta, ta murɗe jikinta. "Ke! Malama ki taso Abba yana kiranki" sai dai shiru Nabilan ba ta motsa ba. Walida ce ta shigo ɗakin tana faɗin ta ga dama ta buɗe ɗakin kenan, sai dai tana ganin irin kwanciyar da Nabila tayi ta ja ta tsaya. A fusace sauda ta tafi ta ɗala mata duka Walida ta ce "Yaya sauda kina ganin irin kwanciyar da tayi, da ƙyar idan ba iskokai za ta yi ba" da sauri Sauda ta ja da baya ta ce "Taɓ wallahi ba zata dake ni a banza ba" Nabila ta saka hannayenta, ta toshe kunnuwanta dan ta daina jin maganar su. Sauda ta koma ta gaya wa Abba, cewar Nabila iskokai ta tayar. Abba ya taso yana yi wa sauda faɗa, a kan cewa ya hana cewa Nabila tana da da iskokai, takura ce kawai ba ta so da ɓacin rai. Ya ƙarasa ɗakin yana kiran sunan Nabila. Ya ɗagota daga kwanciyar da ta yi, jikinta yayi wani irin mahaukacin zafi, har wani huci take yi. Idanunta sun kumbura sun yi suntum, ga wani irin ja da suka yi, ga wasu irin siraran jijiyoyi da suka kwanta a saman goshinta. Sai da Abba ya razana da yanayin da ya ganta, "Arfa, meyasame ki haka? Meyake yi miki ciwo" Ta buɗe baki za ta yi magana, amma bakin ya din ga karkarwa ta kasa furta komai, hawaye ya din ga bin gefen idonta. Ya kalli walida ya ce "Bani bedsheet a rufe mata jikinta" ta duba ta ɗaukko masa, ya rufe wa arfa jikinta, ya din ga tofa mata addu'a. Wani abu mai nauyi, ya tokare mata ƙirji, ya hana numfashinta fita yadda yakamata, a ƙalla Abba ya kai awanni biyu, yana yi mata addu'a yana tofa mata, sai bin sa take yi da ido, amma ta kasa magana, sai can wani irin nananuyan bacci ya ɗauke ta, dan ba ta yi bacci ba jiya gaba ɗaya. *** Walid ne yake ta kokowa da Al'amin, a kan lallai sai ya fita ya kai kansa wurin 'yan sanda, a sakar masa liti, shi a kama shi, amma kafin nan sai ya fara kashe Nabila. "Ita wannan da tayi maka abun da bai taka kara ya karya ba zaka kashe, ko kuma zaka fuskanci indabo da madaki ne ka bar maganar wannan ƙaramar alhakin?". Viper ya ɗaga rinanun idanunsa jawur da su ya ce "Zuwa yaushe? Zuwa yaushe mutane za su daina cutuwa a dalilina? Ba zan sake gangancin da na yi a baya ba, dole a saki liti, in dai kai kaina zai saka a sake shi" "Is a minus case, dole zai fita, amma bama buƙatar a sake kama ka, ka gane mana, dole mu shirya ɗaukar fansar ka" Viper ya sake kallon Walid ya ce "Sai na kashe yarinyar nan fa" "Indabo yakamata ka kashe da Madaki, wani tunanin yakamata ka yi a kan wannan yarinyar ba wannan ba" "Tarko aka yi mini da ita, ko ba ka gani?" Walid ya girgiza kai ya ce "Haryanzu bamu da tababcin hakan, amma ba ka da wani sharhi ko tunani a kanta?" "Babu, idan na sake ganinta kuma sai dai wata ba ita ba" ya bashi amsa kai tsaye. "Shikenan, yanzu dai zan fita in ga me za ayi a sako mana liti". Viper yayi shiru bai ce masa komai ba, sai da ya yinƙura zai tashi, Al'amin ya riƙe shi. Walid ya juyo ya kalleshi ya ce "Ina alƙawarin da ka yi mini?" Walid ya ce "Ina sane, haryanzu kayan ba su sauka bane ba, ka san yanzu hanyar akwai tsaro sosai ba irin na da bane ba" "Bani wanda ka kwashe ka fita" Cikin damuwa walid ya ce "Wai dan mai zamani so ka ke yi sai ka haukace ne gaba ɗaya hankalinka zai kwanta, wannan uban ƙwayoyin da ka ke jibgaw kanka ba abun da suke yi maka, jikinka duk ya riga ya bujire, ka yi haƙuri mu bi a sannu" "Mai laya..... Walid ya ce "Mai zamani" "Ka yi mini abun da nake so, ai na riga na daɗe da gama haukacewa, ka bani idan na cigaba da zubawa na san za su yi mini" Walid ya girgiza kai ya ce "Da za su yi maka, da tuni sun yi, ka yi haƙuri ka bani lokaci" Al'amin ya waro masa idanunsa ya ce "Ka fara kaini bango, baku san fa me nake ji ba, bana bacci, ƙwaƙwalwata so take ta tarwatse, sonake komai ya shafe daga cikin kaina, ko da hakan yana nufin zan haukace" "Fansar ta ka fa" "Zan ɗauka" Walid ya yinƙura zai fice ya bar Al'amin, amma ya sake riƙe shi, Walid yana ƙoƙarin ƙwacewa, hakan ya ƙara tunzura Al'amin, ya fara ƙoƙarin shaƙe Walid. Babu yadda Walid ya iya, duk da yadda Al'amin yake zuba wa kansa kayan maye, amma yafi ƙarfin sa, ya dunƙule hannu, ya daki jijiyar wuyan Al'amin, ya silale ya faɗi ƙasa. Yayi sauri ya durƙusa a kansa, ya ga Al'amin yana ta ƙifta idanunsa, bai kai ga suman ba, jikinsa ya saki gaba ɗaya. Walid ya dafe kai yayi shiru, abubuwa na neman su ƙwace musu, gashi alamu sun fara nuna ƙwaƙwalwar Al'amin na nema ta fara taɓuwa. Ya dafa kafaɗar Al'amin ya ce "Ka ƙara bamu lokaci ɗan uwa, zamu kawo ƙarshen komai, da yardar Allah" ya tashi ya fice. *** Abba da magajiya sai anty, su ne suka yi ta ɗawainiya da Nabila, har ta ɗan samun nutsuwa, take ta uban bacci, tana tsaka da baccin sumayya ta zo, dan jiya hankali a tashe ta kwana, ta jirata har ta gaji, taje can wurin aikinta an ba ta je ba, ta zo gida an ce ba ta zo ba, ga lambobinta ba sa shiga, ta din ga fargabar Allah ya sa ba su indabo ne suka yi mata wani abun ba, gashi suka din ga kiranta suna tambayarta ta gaya musu me suka tattauna da Nabila. Yanayin da ta ga Nabila, ya tsoratata, gaba ɗaya kamar ba ita ba, duk ta yi wani iri. Cikin ikon Allah ta farka daga nannauyan baccin da ya kwasheta, da sumayya ta fara tozali, cikin kulawa sumayya ta ce "Sannu" ta jinjina mata kai kawai. Duk shegen surutu irin na Nabila, sai bakin ya mutu, ta kasa cewa kowa uffan. Sai da suka kaɗaice, sannan sumayya ta ce "Nabila ki yi magana mana, meyafaru da ke? Kiran me ki ka yi mini kina so mu haɗu? Kuma na neme ki na rasa jiya, yau kuma na ganki a haka ko wani abun ne ya faru?" Nabila ta ƙura mata ido, yanzu ita ta ina za ta fara yi wa Sumayya bayani ma, wataƙila idan ta bata labarin abun da ya faru ma ƙaryata ta zata yi, ta ce mata ba ta da hankali, ta san babu lallai ta bata goyon baya, a kan abun da take niyyar yi. Ba wannan ba shi kansa Nasir idan ya dawo, ta ina za ta bi ta warware mugun ƙullin da tayi, muddin ta yarda aka kama Viper a sanadinta, ta zama azzaluma duk da ba ta ji ƙarashen labarin ba, amma yin hakan shiga hakkinsa ne. Sumayya duk yadda ta kaɗa ta raya, fafur Nabila taƙi cewa komai, hasali ma zancen zuci ta din ga yi taƙi kulata. Abba ya din ga yi wa Nabila faɗan yawo ba ɗankwali, jin kaɗe-kaɗe da kuma yawan kwalliya. Walida ta shigo da waya a hannunta, ta miƙawa Nabila ta ce "Gashi Yaya ne zai yi magana da ke" Nabila ta girgiza mata kai, ba zata karɓa ba. "Me zan ce masa to?" Sumayya ta karɓi wayar suka gaisa da Nasir ta ce "Yaya mutuniyar jikin ba daɗi, taƙi magana ma gaba ɗaya, ka yi haƙuri ko zuwa anjima mu gani idan zata yi" Ya ce "Shikenan, hanklina ne a tashe, ban ji ɗuriyarta ba ai, na sake kira anjima". Suka yi sallama ta kashe wayar. *** Kwanaki kusan uku ramma na fama da jikinta, kafin ta ɗan ji ƙwari, a kwanaki ukun nan, Abdul bai kulata ba, zai dai ba ta abinci ya bata magani, sai a kwana na uku da ya ga yi ƙwari, har tana salla. Tun da rana ta fara ganin take-takensa dan haka hanklinta ya ƙi kwanciya, da daddare ta kasa bacci sam, aikuwa kamar yadda ta yi tsammani, sai gashi ya shigo ɗakin, yana miƙa yan kallonta. Cikin hanzari ta tashi tsaye. Ya mayar da ƙofar ya rufe ya ce "Ina zaki ne?" Ta hau ja da baya, ya nufota gadan-gadan kawai ta ciro wuƙar yanka fruit, ta ce "Wallahi ka taɓani sai na caka maka, sai na kasheka azzalumi mara imani kawai" Ya ce "Ohh wow, in ajiyeki ina ciyar da ke, ki ɗauki wuƙa ki ce zaki kashe ni, ni da ki ka samu ban kashe ki ba? Dole na canza taku. Ya danƙota sai ga wuƙar a hannunta, amma ta kasa yi masa komai da ita, ba ta wuƙar yake yi ba, ya fara ƙoƙarin yi mata abun da ya saba, taƙi sakin wuƙar, garin kokowar ƙwatar kanta ya yanke shi da wuƙar hannunsa. Sakin wuƙar ta yi ta ce "Na shiga uku" ya tsaya yana kallonta, hannunsa na zubar da jini. Tayi sauri ta saka hannunta, ta danne wurin da yake ta zubar da jinin, ta ga hakan ba zai yi ba, ta kama rigar jikinta tana dannewa tana cewa "Ka yi haƙuri" ya ƙura mata ido, gaba ɗaya sai ta rikice. "Ni zaki kashe ko?" "A'a ba kasheka zan yi ba, sonake kawai ka ji tsoro ka ƙyaleni, ka yi haƙuri" ya fizge hannunsa ya fice, ta samu wuri ta zauna hankalinta rabi a tashe, rabi kuma tana gode wa Allah da ya saka ya ƙyaleta. Nabila ta warware, sai dai gaba ɗaya walwalarta ta ragu sosai da sosai, ba ta iya bacci, tunaninta da lissafinta kawai yaya zata ɓullowa lamarin. Ta sake ɗaukko wayarsa tana jujjuyawa, ta tuna abun da Walid ya ce mata "Sai dai ki je shi ya ƙarasa miki" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Dole zan je, zan neme shi, sai na ji ƙarshen labarin, for now dole na tsayar da aikin DSP, na kamo bakin zaren nan, dan gudun kar a haihu a ragaya. Ranar monday ta kunna wayarta, ta shirya ta ce wurin aiki zata tafi, ana ta zancen Nasir zai dawo, sai dai ko a jikinta, dan ba ta shi take yi ba, ta shirya ta fice. Da ƙafarta take ta tafiya, dan kar ta hau abun hawa tayi saurin zuwa wurin aiki, ba ta gama tunanin da take son yi ba, wataƙila ko za ta samu mafita a haka. Kamar an ce ta waiwaya, ta ga wata baƙar mota, na ta bin ta sannu a hankali, tun da ta fito titi kuma ta ga motar, ta basar ta cigaba da tafiya, bayan wasu mintuna ta ƙara waiwayawa ta ga motar still tana bin ta. Tsayawa tayi ta juya ta nufi motar, sai aka tsaya aka yi parking aka daina bin ta, glasses ɗin motar tint ne, dan haka ba ta ganin na ciki. Ta ƙarasa ta hau ƙwanƙwasa glass ɗin, amma ba a sauke ba. Ta gaji ta tari abun hawa, ta tafi. Ta shiga reception kenan, ta tarar da wasu matasan  mata su biyu, a cikin tashin hankali. Ba ta damu ba ta wuce su, ta tafi office ɗin ta, ta ajiye kayanta ta sake fita harabar wurin, ta gansu a tsaye suna kuka. Har ta gota su ta dawo, ta kallesu ta ce "Lafiya kuwa?" Ɗayar ta ce mata "sannu" Nabila ta ce "Yauwwa meyafaru ne?" "Dama babanmu aka yi wa sharri, an kai shi wurin 'yan sanda ma, wai kotu za a kai shi, an ce mu ɗaukar masa lawya mai zaman kansa, mun ji ba zamu iya ba, abun da tsada sosai" Nabila ta ce "Sharrin me?" "Gadi yake yi a wani gida, sai ɗan wan matar gidan ya yi wa mai aikinta fyaɗe ya gudu, su suka fara kaita asibiti, da shi mai wankin gidan, shi ne daga baya aka kama su, wai su ne suka yi mata" Nabila ta yi shiru tana nazarin maganar ta kalli ɗayar ta ce "Yayata kin tabatta, ba na shiga case ɗin mutumin da ba shi da gaskiya, kar na yi bincike na tarar da saɓanin abun da ku ka gaya mini" "Wallahi ba ƙarya muka yi miki ba" Ta ce "Well, yanzu ina da tarin ayyuka a office ɗina, personally zan taimaka muku, ku zo gobe in Allah ya kaimu ƙarfe tara na safe, zamu je wurin mahaifin naku, na ga abun da zan iya yi a kai" Godiya suka din ga yi mata, tamkar za su durƙusa mata, yanayinsu kawai ya nuna suna fama da matsin rayuwa. Ta so haɗuwa da barrister Habib, amma bai shigo ba, ya tafi gudanar da wasu shari'oi dan haka ta zauna ta gudanar da nata ayyukan. Sha biyu na cika, ta ɗauki jakarta ta fita, kiran Nasir ya shigo wayarta, kamar ta share, sai ta ɗaga tayi sallama. "Barrister, kina office ne na biyo?" "Ka dawo kenan?" Ya ce "Eh ina cikin kano" Nabila ta ce "No, zan yi wata shri'a ne, ka je gida ka huta na kusa dawowa nima" ba ta jira mai zai ce ba, ta saka wayar a Flight mode, ta tari abun hawa, ta nufi unguwar da Viper yake. Ayshercool 08081012143 47 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Suna tafe a hanya, Nabila na ta saƙe-saƙe daban daban a cikin ranta, har suka iso dai-dai in da ta sauka wancan zuwan, ta sallami mai napep ɗin, ya din ga kallonta yana tunanin ita kuwa me za ta yi a irin wannan wurin haka ranar tsaka. "Malam lafiya, ka tafi mana" ya ce "To, tafiyar zan yi" ya ja baburinsa ya tafi. Sannu a hankali ta bi waccan hanyar da Walid ya bi da ita wancan karon, amma ta kasa gane hanyar da suka bi, balle ta gano gidan. Ta din ga nausawa cikin wurin, tana bulayi, amma ko rabin gano hanyar ba ta yi ba, gashi ta fara gajiya ga rana tana yi. Sosai take bulayi, tana sake nausawa wani wurin, amma sai ta ga ta ɓulla wani wurin daban. "Ke baiwar Allah" ta ji muryar wani a bayanta, ta waiwayo tana kallon mutumin, sanye da uniform ka security. "Me ki ke yi a nan wurin rana tsaka haka?" Ta ce "Dan Allah malam wani gida nake nema" Ya kalleta ya ce "Gida a nan kuma?" Ta ce "Eh" "Gida fa ki ka ce?" "Eh wani ƙaramin gida ne, rannan na zo ma amma hanya ta ɓace mini" ya girgiza kai ya ce a'a babu wani gida a nan haka, duk kamfanunnunka ne, sai gonaki, can kuma idan ki ka bu dutse ne, daji zaki shiga dan haka babu wani gida a nan" Nabila ta ce 'Malam akwai gida a nan haka, na je gidan fa" Cikin tsawa ya ce "Ke babu wani gida a nan, ki bar wurin nan tun ban sakar miki karnuka ba, ko na kama ki na haɗaki da jami'an tsaro" Ta ƙare masa kallo ta ce "Ni zaka saka a kama, na yi maka kama da ɓarauniya ne?" Ya ce "To wa ya sani, yanzu ai ɓarayi ne kawai ɓata gari ba, kuma ba a goshi ake ganin ɓata garin ba, ta cigaba da ƙarewa wurin kallo, ba ta ga hanyar gidan ba" ta ja guntun tsaki ta juya ta fara tafiya, sai mamaki take yi, tabbas gidan a nan haka yake, amma ya aka yi haka ta faru? Haka ta koma ba tare da ta gane wurin ba. Tun daga haraba yake murmushi, kamar bakinsa zai yage, cikin ƙarfin hali ta ƙaƙalo murmushin ita ma, ta ƙarasa ta ce "Welcome home DSP" ya miƙa mata hannu, ta miƙa masa na ta suka gaisa ya ce "I really miss you barrister" "Me too, ya aiki?" "Aiki Alhamdilillah, daga shekranjiya zuwa yau duk ina cikin damuwa, an ce ba ki da lafiya, ba kya ɗaga wayata" Ta ce "Ka san ni ɗin ce a lallaɓa, auren zamani, yau da lafiya gobe babu, bari na je na yi wanka na ci abinci" Ya ce "Take your time, ki huta sosai zuwa yamma, zan je office ne, zan ga mutumin da aka kama, aka ce ya san in da Viper yake, kan na dawo ki bani abun da ki ka ce" dammm! Ƙirjinta ya buga, amma ta maze ta ce "Ok bye bye, sai ka dawo" ya ɗaga mata hannu ta shiga cikin gidan. Sai yanzu ta tuna tayi alƙawarin gaya masa wani abu idan ya dawo, wanda dama wayar Viper take son ba shi, wanda a yanzu ko me za'ayi mata ba zata miƙa wayar nan ba, sai ta ji ƙarshen labarin nan. Tana wanka tana zancen zuci, idan ta ce za ta yi wa Nasir bayani, ba ta da wata cikakkiyar hujja, da za ta sanya ya fuskanci in da ta dosa, kuma sai ta tonawa kanta asiri na cewa ta haɗu da Viper. *** Ɓangaren ramma kuwa, tun da ta yanki Abdul da wuƙa, ba ta sake ganinsa ba, har gari ya waye, duk abun duniya ya ishe ta, wai ita ta yi wa mutum illa da wuƙa har ya zubar da jini. 'sai me, ke kin manta abubuwan da ya aikata miki?' wata zuciyar ta tambayeta. 'Duk da haka, da kuma na caka masa in da zai mutu fa?" Ta tambayi kanta. Ta buɗe falon, ta fito da rigarsa sai towel da ta ɗaura, ta rufe jikinta da ɗan kwalin kayanta, ta fito falon ba kowa. Solomon ya fito zai shirya abinci a kan dining, ta ce masa "Ina kwana?" Cikin gurɓatacciyar hausarsa ya amsa mata, ta ce "Yana ina?" Yayi mata saroro ba ya jin hausa. "Kai ba ka jin hausa ne? No hausa?" Ya jinjina mata kai tare da yin murmushi. Hausa da turanci take haɗawa, tana tambayar sa ina wannan mutumin, mai gidan nan?" Turancin nata ya bashi dariya, da turanci ya ce mata bai kwana a gida ba. "Ina ya tafi?" Ya ce "Ba a tambayarsa in da ya tafi" tayi ajiyar zuciya ta kalli, kwanukan abincin ta ce "Duk kai ka ke dafa wannan? A ina ka iya girki?" Ya ce "Catering school na yi, tun ina ƙarami kuma, ina taimakawa mamana wurin yin girki, tana sayar da abinci" Ramma ta ce "Ka san koko?" Ya yi shiru yana kallonta, kwatanta masa ta shiga yi, yayi dariya ya ce "Pap" ta ce "Eh, shi ka din ga yi mini turancin ƙanana yadda zan gane" Yayi dariya ya ce "Ai normal turanci ne, kawai dai pidging ne" a dai-dai lokacin Abdul ya shigo falon, ya tarar da ramma a tsaye, tana magana da solomon tana murmushi. Wani abu ne ya tokare masa wuya, suka ɗago suna kallonsa, tana ganinsa ta haɗa fuska, ta din ga satar kallon hannunsa, da ya naɗe da bandeji. "Solomon, yaushe na zama sa'anka da zan ajiye yarinya ka din ga hira da ita? Kai ka ajiyeta? So kuna shirya yadda za ta gudu kenan?" Da sauri solomon ya girgiza kai ya ce "Ba zan taɓa cin amanarka ba sir, abu ta tambayeni nake ba ta amsa" "Babu ruwanka da ita, idan tambayar ce ta tambaye ni" Ya jinjina kai. "Bar wurin nan" da sauri ya bar wurin. Ya ƙarasa dining ɗin, zai zauna ramma ta tashi. "Zauna ina zaki je? Haɗa mini abinci in karya" Cikin tsananin takaici take bin sa da ido. "Zaki haɗa mini, ko sai na turmusheki na yi breakfast ɗin da ke, 'yar dabar ƙauye kawai, ki na 'ya mace kina ɗaukar wuƙa". "Ni ba 'yar daba ba ce ba, kare kaina nayi yinƙurin yi daga mugu irinka mara imani" Ya ɗora ƙafarsa a kan dining ya ce "Na ji, haɗa mini, ko kuma wallahi na yi abun da na ce" Tuni hawaye ya cika mata ido, ta haɗa masa tea, da doyar ta tura masa gabansa, ta tashi zata tafi ya riƙota, ya ɗaga mata hannunsa na dama, wanda a nan ta yanke shi, ya ce "Da wani hannun zan ci?" Ta tsaya tana kallonsa. "Oya feed me, tun da kin riga kin yi wa hannun illa, idan ba haka ba kin san condition ɗin" babu kalar tsinuwa da zagin da ba ta yi masa a zuciyarta ba. Cike da ƙwarewa a fannin iya rashin mutunci da bariki, haka yake haɗawa da hannun ta idan ta bashi a bakin, yana wani ƙare mata kallo. Sai ƙanƙame jikinta take yi, gaba ɗaya wani iri take jin ta. Ya cinye doyar ya ce ta ƙara masa, a ranta ta ce "Shege jaki" Lomar ƙarshe, ya riƙe hannunta, da yatsunta a bakinsa, kokowar ƙwacewa take yi, amma ya riƙe su a bakinsa yana yi mata kallon 'yan iska a cewarta. Ba ta san lokacin da ta dunƙule ɗaya hannun nata ta ɗirka masa duka a kafaɗarsa ba, ɗan dukan da babu in da ya je, ya saki yatsun yana murmushi, da ƙoƙarin tauna sauran doyar, wani irin mugun kallo take yi masa, tare da goge yatsunta a jikin rigar jikinta, ba ta fargaba ya sake tashi, ya haɗe bakinsa da nata, yana ɗura mata ragowar abincin bakinsa, cikin tsananin jarumta, take naushinsa ta ko ina, amma ya saka hannu, ya danna maƙogwaronta, babu shiri ta haɗiye, ya cikata ya nufi 3seater ya kwanta. Iya ƙarfinta ta zage ta din ga zaginsa, har da kalar wanda ba ta taɓa tunanin ta iya ba, ya lumshe idanunsa ya yi mata banza ya ce "Na san maganinki" Nasir ya ƙarewa liti kallo, sannan ya kalli sageant ɗin da suke tare ya ce "Kana nufin bai yi magana ba gaba ɗaya?" "Eh sir, ya ƙi yi" Ya mayar da idonsa kan liti ya ce "Ka sauƙaƙawa kanka, ka sauƙaƙa mana aiki, ka gaya mana abun da muke tambayarka a kai. Ina Aminu Viper?" "Ban san in da yake ba" "Ƙarya ka ke yi, rahoto ya zo mana a kan ba shi da wasu makusanta bayan iyayensa sai ku, babu iyayensa a lissafi tun da dama sun riga sun sallama shi, ka fi kowa sanin in da Aminu viper yake" Liti ya ce "Tun da ka samu wannan rahoton, kai ka san amanar da ke tsakaninmu ba wadda zan yadda ta rushe ba ce a kan ƙaramar bazarana ba ce. Kalleni da kyau, na yi gwagwarmaya na ga rayuwa, prison ceil, na shiga kala-kala. Kuma ban taɓa zuwa gaban ɗan sanda na yi magana biyu mabanbanta ba, idan zan yi zan yi kawai. Eh ko a'a. Ko kasheni zaku yi a yanzu, ban san in da yake ba" Nasir ya kaɗa kai ya ce "Kar ka cika baki, wataƙila wannan karon, ka zo in da zaka yi magana biyu, ina Aminu Viper yake" Liti ya ziraro harshen sa, kamar yadda Al'amin ya ke yi ya ce "Allah ya ja da ran mahadi mai dogon zamani. Ambaton sunansa kawai, girma muke bashi na musamman. Abun da ba ka gane ba shi ne, shi fa mai gida ya ci dubu sai ceto wallahi. Idan ba haka ba tayaya za a saki mutumin da yake tsare, kuma a dawo ana nemansa? Gangan ma kenan"ya yi maganar yana dariya. Nasir ya ce "Babu laifi, zaka yi magana dan dole" "Magana biyu, abun da liti bai taɓa yi ba kenan, ko wace irin azaba kuwa zaka gana mini, ai ƙarshen ƙwarewar taku kenan, ku yi ta ganawa mutum azaba, ya amsa laifi nasa da ba nasa ba. Idan har manyanka ba su saka na yi magana biyu ba, ba ka da wata izaya da zaka yi mini na yi magana biyu, idan kuwa na yi magana biyu ashe ba yaron Viper bane ni". Wata inkiya Nasir yayi, kamar yadda liti ya faɗa kuwa, aka saka wasu kurata, suka din ga jibgarsa da kulki, kamar sun samu tumu, suka yi iya yin su suka yi masa lilis, sannan suka kai shi wani ɗaki mai duhu suka kulle shu. Gaba ɗaya Nabila tana ɗakinta, tana ta lissafin yadda za ta ɓullowa al'amuran nan da suka sakota a gaba. Ta idar da sallar isha'i, ta zauna a kan daddumar, sai tufka da warwara take yi, gashi ta rasa da wa zata tattauna maganar ta ji daɗi. "Tunanin me ake yi haka ne?" Ta ji muryar Nasir. Tayi ajiyar zuciya ta ce "Yaya sannu da zuwa" Ya zauna a gefen gadonta tare da cewa "Yauwwa arfa, kin ga ban dawo da wuri ba ko? Na je na ga mutumin da ki ka yi mini bayani, na saka aka kama, ta tabbata yaron Aminu Viper ne, amma riƙaƙƙen mara mutunci ne, ya ƙi magana, duk wani nau'i na tuhuma an yi masa amma ya ƙeƙashe ƙasa yaƙi magana". Nabila ta ce "Ikon Allah, bai faɗi in za yaken ba kenan?" Ya girgiza kai ya ce "Bai faɗa ba. Amma muna nan muna trying, alamu sun nuna ya sani, ɓoyewa yake yi. Yauwwa yanzu gaya mini me ki ke son ki gaya mini lokacin bana nan" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Nothing much, dama dai duk a kan case ɗin nan ne, na ce me zai hana ka bibiyi case ɗin daga tushe, misali daga gidansu, iyayensa mutanen kewayen da ya zauna da su". "Me hakan zai amfana?" Yayi maganar yana kallonta. Ta ce "Kawai ji nake kamar akwai lauje a cikin naɗi, a kan sha'anin Aminu Viper, kamar abun da aka baka a kansa is not complete, something is missing, yakamata a fara samo full details na abun da ya faru". Ya girgiza mata kai ya ce "Duk bani da isashshen lokacin yin haka, na yi ƙoƙarin yin hakan, aka ce ba shi aka sakani ba, kuma duk maganar nan da ki ke yi is a very long way, gara shortcut, idan ya zo hannu muka gama da shi, kotu zamu tura shi, a can ne aikinki yake idan ma tssya masa zaki yi" tayi murmushi ta ce "Hakan fa zai iya sawa na yi suna ko?" Yayi dariya ya ce "Ke dai kin damu da maganar yin sunan nan, gaba ɗaya kin canza, ko dai haryanzu jikin ne? Gaba ɗaya kin rage ɗokin case ɗin Vipern ma, ko akwai wani abu ne ki gaya mini " ta girgiza kai ta ce "Babu komai" Ya ce "Are you sure?" Ta jinjina masa kai, ya tashi tsaye ya ce "Ban yarda iya abun da ki ke son gaya mini ba kenan, akwai abun da ki ke son gaya mini ki ka fasa, amma da sannu zan gano menene da kaina" Shiru kawai ta yi tana murmushi ya fita, yana ƙoƙarin fita daga falon, ya ci karo da mama, sai da ya ɗan tsorata ya ce "Mama" "Me ka ke yi a ɗakinta da daddaren nan?" Tayi maganar rai a ɓace. Ya ce "Subhanallah, dan Allah mama kar ki kawo komai a ranki, muna magana ne a kan aiki... "Rufe mini baki, aikin banza da na wofi, sai ubanka ya farga ya fara yi maka terere a cikin gidan nan ko, kana zuwa ɗakinta da daddare, ka dai san ita ba zai tagayyarata ya nuna laifinta ba sai kai. Duk lokacin da na yi ƙoƙarin fahimtar da kai, irin wannan abun ba ka gani, daga dawowar ka, zaka fara sakani magana saboda wannan sheɗaniyar yarinyar ko Nasir? Ka cigaba ban ce ka fasa ba" ta nufi ɗakinta ta bar shi a tsaye a wurin saroro yana kallonta. *** Ramma tana kwance ta sha kuka har ta gaji, tunanin halin da mamanta take ciki kawai take yi, ta san tana can hankalinta a tashe, tana faɗi tashin neman in da take. Ta gaji da kwanciyar, ta ɗauki ruwan da yake ajiye, a kan side bed, ta sha fiye da rabi, saboda maƙogwaronta duk ya bushe, saboda kukan da ta sha. Ta kwanta tana jiran bacci ya kwasheta, amma bacci ya gagara, sakamakon wani irin yanayi da ya din ga bijiro mata, har wani irin gumi take yi, ta tashi cikin matsananciyar damuwa, amma ta rasa takaimaimai meyakamata ta yi. Ta nemi wuri ta kwanta, ta takure, tana ta mamakin wannan wane irin abu ne haka. Abdul ne ya shigo yana fito, tayi shiru ba ta motsa ba, ya nemi wuri ya kwanta a bayanta. Ba ta yi masa tashin hankali ba, ko ƙoƙarin yin gardama ba, babban abun da ya ɓata mata rai, ya sanya ta ji tamkar ta kashe kanta, bai wuce yadda ta iya biyewa Abdul ba, ta tabatta mazinaciya!. Kuka take yi iya ƙarfinta, har da sheshsheƙa ko a jikinsa, kaɗa ƙafa kawai yake yi, daga baya ya tashi zaune yana kallonta, yayi dariya ya ce "Ba dai ke taurin kai ba, ai na san maganinki, you are very healthy and unique, zaki yi mana baƙin ciki. Ba kya buƙatar komai kan ki yi functioning lafiyayyiya ce ke, amma tsinanane taurin kai irin na ɗan ƙauye ba zai bari ki yi abun da ya dace ba". Ya ɗago wata ƙwaya ya ce "You force me to use it on you. Idan ki ka bari muka cigaba a haka ke zaki sha wahala, dan zata iya cutar da ke, aikin gama ya riga ya gama ba wani sauran amfani da zaki yi, ni ban ga abun ƙi ko damuwa ba. Na aika a gaya wa babarki ta daina nemanki na ajiye mata ke a in da ya dace". Cikin kuka ramma ta ce "Ba zan taɓa yafe maka ba, Allah ya isa, mazinaci mugu". Ya ce "Mazinata dai har ke" "In sha Allah ba zaka gama da duniya lafiya ba" Ko a jikinsa ya ce "Idan Allah ya nufa na gama da ita lafiyan, sai ki hana ai" ta cigaba da kuka, shi kuma ya juya ya hau bacci. Ta bi shi da kallo, ba ta tunanin ko wankan janaba yana yi, sai da tayi mai isarta, ta tashi ta yi wanka, ta saka wata jallabiya, ta leƙa fuskarsa, ta ga bacci yake yi sosai. Ta lallaɓa ta fita daga ɗakin, ta fara laluben ƙofar fita, sai dai ta nemi hanya ta rasa. Ko ina a rufe ta girgiza manyan ƙofofin, amma ko motsi ba sa yi, ta zauna a falo, ta cigaba da kuka, ta din ga jin haushin karnuka, tsoro yakamata, ta tashi ta koma bedroom ɗin, ta tarar da shi a zaune yana danna wayarsa. Ta nemi wuri ta kwanta a ƙasa. "Idan ki ka kuma yinƙurin guduwa, sai na bar garin nan da ke, ba garin nan ba kawai, zan iya barin ƙasar nan da ke, babu wanda zai sake jin ɗuriyarki, gara ki shiga hankalinki". "Ai ba zan tabattar da kai tabattacen azzalumi bane, sai ka rabani da duniyar" ya kalleta, kamar ba daga bakinta maganar ta fito ba. Duk a yawon barikinsa, babu karuwar da ta isa ta ci masa mutunci ko ta zage shi, amma a garin kwashe-kwashensa, ya kwaso 'yar mitsitsiyar yarinya tana cin zarafin sa, yayi mata shiru, yana jin ta tana yi masa Allah ya isa ƙasa-ƙasa har da Allah ya tsine masa, amma ya shareta, tun da yau ya samu abun da yake so. Nabila tana office ɗin ta a zaune, tana ɗan danna system, sai dai hankalinta ba a kan system ɗin yake ba. Aka danna ƙarrarawar office ɗin, ta bada umarnin a shigo, matasan matan nan ne, wani masinja ya rako, ya ce "Hajiya Nabila, ga baƙi kin yi" Ta ce "To na gode sosai. Bisimillah ku zauna" suka zauna tare da gaida Nabila. A kallo ɗaya zaka ga Nabila ta yi kalar mata masu izza da jin kai, amma kuma kana zama da ita zaka ga saɓanin hakan. Suka gaisa ta ce "Jiya ina sauri zan fita, mun fara magana bamu ƙarasa ba, duk da yau ɗin ma ina son fita ne" Ɗayar ta ce "Ai mun gode ma saurarmu da ki ka yi. Lauyan gwamantin sai yawo yake yi mana da hankali, aka ce mu ɗaukar wa baban lauya mai zaman kansa kawai, mun zata abun mai sauƙi ne, ashe yafi ƙarfinmu". Nabila ta yi musu tambayoyi, ciki har da in da aka ajiye mahaifinsu, ta yi musu alƙawarin za ta je da kanta, ta tattauna da shi, za ta bibiyi komai, kafin a shiga zaman kotu. Suka yi ta yi mata godiya, ta ce "Kar ku damu, ku bani lamabar wayar da zan iya samunku" Suka bata, ɗayar ta ce "To ƙanwata nawa ke zamu baki?" Nabila ta ce "Karku damu, ku yi mini addu'a kawai, akwai abun da na saka a gaba, Allah ya sa na yi nasara baki ɗaya, da case ɗin ku da ɗaya abun da na saka a gaba" da suka fara yi mata addu'a, sai da ta fara jin nauyinsu, dan tamkar ta yi musu bushara da mahaifinsu ya fito, suka hau yi mata hira da labarin yadda sunan mahaifin na su ya ɓaci, a cikin unguwa. Tayi ta basu ƙwarin gwiwa, da tabbacin da yardar Allah za su yi nasara. Bayan tafiyarsu, kawai ta yi wani tunani, ta ɗauki jakarta ba ta zame ko ina ba, sai wurin aikin sumayya, ba ta tarar da ita ba sai Lawisa, sai zuba iko take tana hura hanci. Nabila ta yi murmushi ta ce "Anty lawisa, Sumy ta shigo kuwa?" Ta ɗaga kai da ƙyar ta kalli Nabila ta ce "Eh" "Tana ina?" "Recording take yi". Ta ce "Ok, bari na jirata a nan" tayi maganar tana ƙoƙarin zama. "No please, ba na son takura, ko zaki jirata a reception?" Nabila ta ce "Ba zan iya zaman reception ba, kujerun ba su da daɗin zama a nan zan zauna" tayi maganar tana zama a kan kujerar office ɗin. Baki buɗe lawisa take kallon Nabila, ta maze ko a jikinta, ta na danna wayarta. Ta kalli lawisa ta ce "A kan kujera kawai na zauna, ba hira na ce mu yi ba, 10-20 minutes, ai is not that much da zaki ce ba kya son takura" ta cigaba da danna wayarta. Bayan mintuna goma sha biyar, Nabila ta ji yo muryar sumayya, ta ɗauki jakarta ta fice, ba tare da ta sake kula lawisa ba. Sumayya na ganinta ta harareta, Nabila tayi murmushi ta ce "Haba masoyiyya daina hararata mana" "Matsa ko na make ki, ni ki ka yi wa wulaƙanci ki ka daina ɗaga wayata" "Ba haka bane ba, ayyuka ne suka yi mini yawa, daga nan ma wani wuri zan je na ce bari na biyo mu yi magana" Suka shiga wani office da babu kowa suka zauna, Sumayya ta ce "Wai ni me zaki gaya mini last week ne? Ki ka shanya ni da yake ba mutunci ne ya ishe ki ba, wayarki ma gaba ɗaya ta daina shiga, har gida na je ina nemanki" Nabila ta kaɗa kai ta ce "Aiki ne ya zo mini unexpected, mun je court ne, ina da shari'a kuma zan ga wasu clients ɗina. Dama a tsakanin lokacin nayi tunanin zan iya squeezing time ɗina, mu haɗu, kuma bai yiwu ba". Sumayya ta ƙare mata kallo tayi murmushi ta ce "Ko dai kin sake komawa wurin Aminu Viper ba?" Nabila ta yi murmushi ta ce "Kina zargin na koma ne?" "Na san hali zaki aikata ai, ina gargaɗinki a kan kasada da rayuwarki Arfa" Tayi murmushi ta ce "Ina ma zan iya jin maganarki" Sumayya ta ce "Baki yadda ba kenan?" Nabila ta ce "Mu bar maganar nan, ni wani taimako nake son ki yi mini " Sumayya ta ce "Ina jinki" "Ke ce uwar neman labari, bincike nake son yi a kan honorable ma'aruf Indabo" Sumayya ta kalleta ta ce "Kamar yaya?" "Kamar yadda na gaya miki, taimaka mini nake son ki yi, ki binciko mini duk wani labari da yakamata a kansa" "Me ku ke so ku mayar da ni ne daga ke har shi?" Nabila ta ce "Shi wa?" Sai kuma sumayya ta farga da katoɓarar da ta kusa tafkawa. "Indabon yayi miki wani abu ne?" Sumayya ta ce "No kar ki damu, haushi ki ka bani ne, kin ce Naja'atu Bunkure, kin ce Aminu Viper yanzu kuma kin ce Indabo, Nabila me ki ke son ki zama ne?" Nabila ta tashi tsaye ta ce "Zan je wani wuri yanzu, Ina jiranki dan Allah sumayya, da tarihinsa da tarihin siyasarsa komai da komai da yakamata ina son sani a kansa" Sumayya ta ce "Wai me zaki yi da shi to?" "Amfani mai muhimmancin gaske, sai anjima, ki gaida umma zan zo har gida na gaisheta, kwana biyu ba mu gaisa ba. Ina jiranki dan Allah" ta ɗauki jakarta ta yi waje. Kamar ta tafi gida, sai ta fasa ta ɗaukar mai napep, ta tafi police station ɗin da aka ce mata dattijon nan yana tsare, da ta je ta tarar an canza masa wuri, an mayar da shi sashen kula da manyan laifuffuka. ID card ɗin ta kawai ta nuna, aka bata damar ganinsa, aka fito da shi, dattijo ne amma ba tsoho cancan ba. Suka gaisa ta ce "Baba ni ce, wadda 'ya'yanka suka same ni, a kan maganarka, yaya meyafaru?". Nan ya ba ta labarin duk abun da ya faru, ta ce "To baba yaya sunan shi ɗan yayar matar?" Yayi shiru ya ce "Wallahi ban sani ba, yana dai zuwa gidan da yake ban daɗe da fara aiki a wurin ba" Ta ce "Yanzu ina ne gidan da ka ke aikin, sannan ina yarinyar take, dole zan ganta " Ya share hawayensa ya ce "Wallahi ban sani ba" Nabila ta tambayi 'yan sandan suka ce sai dai ta koma can in da aka fara binciken case ɗin" Ta ɗauki bayanan da zata ɗauka, ta yi musu sallama ta tafi. *** Kasancewar Abdul da wuri ya fita, solomon ma baya nan, Ramma ta din ga yawo tana neman hanyar fita tana kuka, amma ta rasa, tayi-tayi ta samu hanya ta rasa, ƙarshe ta koma falo ta zauna tana kallon Tv. Wata magazine da tarin takardu ta gani, ta ɗauka tana kallo, signing ɗin sa mai kyau, Abdul yassar ma'aruf Indabo. Shiru ta yi tana tunanin, kamar ta san sunan nan. Ƙofar falon ya saka key ya buɗe ya shigo, yayi sallama ta amsa a hankali, sai dai yayi kissing ɗin kumatunta sannan ya zauna, ta tsuke fuska tana matsawa. Ya kuma matsawa kusa da ita ya ce "Kin ci abinci kuwa?" Ta yi masa shiru. Ya ɗago mata jakar hannunsa ya ce "Yakamata ki san menene a jakar nan" taƙi kula shi. Ya buɗe jakar, ya zazzage mata, kayanta ne a ciki, da kuma wasu sababbin kayan ya sayo mata. "Babarki tana gaishe ki" Ta kalleshi idonta fal hawaye ta ce "Me ka ke nufi?" "Na ce ta sallama mini ke, ba sai ta cigaba da nemanki ba" Ta sake kallonsa ta ce "Waye indabo?" Ayshercool 08081012143 48 Ya kalleta ya ce "Meye alaƙarki da sunan? Kin san shi ne?" Ta girgiza masa kai alamar a'a. "To a ina ki ka ga sunan?" Ta ɗago masa takardar ta ga signing ɗin sa, da full name ɗin sa. Ya ce "Well babana ne, ba abun mamaki bane dan kin san shi, ɗan siyasa ne" Cikin rauni ta ce "Me ka ce wa mamana da ka je?" "Ba na gaya miki ba, na ce kar ta sake nemanki, kin zama mallakina" "Saboda ba ka da tausayi da imani ko? Wallahi idan baƙinciki ya kashe mahaifiyata ba zan yafe maka ba" "Ikon Allah, me zai sa baƙin ciki ya kasheta, na kai mata kayan buƙata a matsayin ina tare da 'yar ta. Ku ne haryanzu ku ke wannan kidahumancin, kun ƙi ku waye, turawa duk in da mace ta kai 18yrs tana da ikon zuwa in da take so tayi rayuwa, amma ku da an yi magana sai ku ce aure aure, in anjima kuma ku yi ta surutun wahala ku ke sha a auren" Ramma ta ce "Saboda yahudanci ko? Mu ai ba turawa bane, musulmai ne baƙar fata, hausawa masu riƙo da addini da al'ada. Ni ban shekara sha takwas ɗin ba, idan ma na yi ai sai da yadda ta da amincewa ta. Kawai saboda bamu da kuɗi ka yi mini fyaɗe ka je har gidanmu gaban uwata ka ɗaukko ni, ka rabani da ita, kuma ka koma ka karɓo kayana ka ce mata ta daina nemana kai ba aurena ka yi ba, kai ba wani abu ka yi da zaka taimaki rayuwata ba, ka ɗauki hakkinmu ba ka yi mana adalci ba" Ya ce "Ke kin isheni, sai ka ce ke kaɗai ce 'ya? Ni fa ban taɓa ɗaukar wata mace na ajiye ina lallaɓata ba sai ke, kuma ma ku da ake haihuwar ku barkatai babu tsari, har wani damuwa za a shiga dan an ɗauki ɗaya? Kashe ki fa na yi niyyar yi na ƙyale ki". "Mu ba ai haife mu barkatai ba, mu uku ne, yayanmu ya rasu, ƙanina ba shi da cikakkiyar lafiya, ni kuma ka ɗauke mata ni, ban da dalilin maraici babu abun da zai saka ka ganni a birni aikatau, har ka keta mini haddi, bayan ka turo mana wata azzaluma, da fari ta ce zata taimaka mini, ta koma gaya mana yahudanci, ka ɗauke ni a gaban uwata, ka zo ka mayar da ni karuwa ka yi wa kanka adalci dan Allah kuma nima ka yi mini?" "Naja'atu Bunkure ba ƙarya ta gaya miki ba, tun a lokacin da ba ku nuna taurin kai ba, da ba a zo nan ba, ku ku ka janyo koma menene ai" Ramma ta haɗa hannayenta biyu, ta rufe fuskarta tana kuka ta ce "Ka cuce ni, ka lalata mini rayuwa, dama kasheni ka yi na huta, ka wulaƙanta rayuwata a matsayina na 'ya mace musulma da addinina ya suturta. Da ƙanwarka ce ni ko 'yar ka, ba zaka zuba mini ido ka ce na je na yi tarayya da wani ba aure ba, kayi amfani da kuɗi, ka wulaƙanta ni dan ni 'yar talaka ce ba ka kyautawa rayuwata ba" ga ta yarinya ƙarama, sai iya tsara magana. Abun da bai taɓa ji ba sai a wannan karon, kukan ramma a cikin zuciyarsa, maganganun ta suka tsaya a zuciyarsa, amma a zahiri ya nuna ko a jikinsa, ya tashi ya bar ta a falon ya tafi ɗaki. *** Ɗan mama yana ta kaiwa yana komowa, tsakanin ɗakin Viper da tsakar gida, yana jiran Walid ya fita, amma ya ƙi fita ya zauna ba shi da niyyar fita. Viper kuma sai bin ɗan mama yake yi da ido. Walid ya ce "Kai ɗan mama, kamar ba ka da gaskiya" Ɗan mama ya ce "Haba Oga walid me ka gani?" "Ba sai na gani ba, alamun hakan na gani, wallahi na ga abun da bai yi mini ba, sai ranka yayi mugun ɓaci" Ɗan mama ya ce "Kar ka damu Oga walid, babu wani abu da zaka gani wanda zai ɓata maka rai" Walid ya jinjina kai, ya cigaba da shan sigari. Al'amin ya yinƙura ya tashi, Walid ma ya tashi ya ce "Ina zaka?" Al'amin ƙura masa idanunsa da suka yi wani irin mugun jaa. "Ba wai tuhumarka nake yi ba, ko wani abu ba, kawai dai ba na son ka yi wani abu da zai wargaza mana shiri ne" "Iska zan je sha, ko yau ma yinƙurin kashenin zaka yi?" Walid ya girgiza kai ya ce "Last time ɗin ma, ni ba niyyar kasheka na yi ba, ƙoƙarin hanaka abun da ka yi niyya na yi, a dawo lafiya" Al'amin ya nufi ƙofar fita, ɗan mama ya ce "Oga Viper, bari na zo mu je na taka maka" Walid ya riƙe rigarsa, ya tsare shi da ido. Ya sosa kai ya ce "Dama raka shi zan yi" Al'amin bai waiwayo ba, kawai ya fita, Walid ya fara saka hannu a aljihun ɗan mama yana caje shi, Ɗan mama ya riƙe hannunsa ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri zan yi maka bayani". "Sakar mini hannu, ko na kwaɗa maka mari" Ɗan mama ya sakar masa hannu ya ce "Amma dai da ka tsaya na yi naka bayani" Walid ya ciro baƙar leda a aljihunsa, ya buɗe, ampoules ɗin allura ne da sirinji, sai baƙin capsule. Walid ya kalleshi, ɗan mama ya ce "Wallahi cewa yayi sai na nemo masa su, idan ba haka ba, ba ya iya bacci, kansa zai fashe ni kuma sai ya bani tausayi, daga ƙarshe kuma ya ce wallahi idan ban samo masa ba sai ya kashe ni" "Sai ya kashe ka, kai ka taɓa ganin ya kashe wanin?" Ɗan mama ya girgiza kai. "Wallahi idan ka kuma sayo wannan hard drugs ɗin ka kawo masa, sai na saka maka ƙarfe ka ji na rantse" ɗan mama ya ce "To, amma dan Allah shi ma ka gaya masa, ka san idan na ce masa a'a ba zai yi mini da daɗi ba". Walid ya ce "Idan ya ce ka kawo masan, ka ce masa to, ka gaya mini" ya jinjina masa kai. Viper yana zaune a kan dutsen, ya zubawa wuri ɗaya ido, kansa kamar ya tarwatse haka yake ji, ga ƙirjinsa kamar an ɗora masa dutse, da ƙyar yake iya numfashi, ga jikinsa sam babu ƙwari, banda kashe masa jiki babu abun da ƙwayoyin nan suke yi, soyake yayi bacci mai sunan bacci, ko ya manta komai da yake cikin ƙwaƙwalwarsa amma abu ya gagara. "Madaki! Indabo!" Ya faɗa a hankali yana sunkuyar da kai, ya ɗaga kai kamar a mafarki ya hangota, ta sauka daga adaidaita sahu, sai waige-waige take yi, yana saman dutsen sosai, dan haka yana hangota. Ta tsaya tana kallon hanya, in da yake take facing, amma ita ba ta ganinsa. Dogon hijjabi ne a jikinta yau, a hankali take tafiya tana cigaba da waige-waige, mamaki ne ya kama shi, me kuma ya dawo da ita wurin nan yau? Zuciya ce ta tinziro shi, ya ji kamar ya sauka ya je ya naɗa mata shegen duka. Mata halin su ɗaya, cin amana 'yar madarar sa ce kawai ta fita daban sai umminsa, ta sace masa waya ta gudu, ta saka an kama liti, saboda tsagwaron rashin kunya ta sake dawowa, ko uban me ta dawo yi oho?. Hakan ya ƙara tabattar masa he's not safe, za ta iya kawo jami'an tsaro su kama shi, sai dai kash, shi ba ya fargabar a kama shi, a kama shi ko a ƙyale shi, shi ba wannan ne a gaban shi ba yanzu. A yau ma ba ta iya gane hanya ba, bulayi take ta yi, tana nema, amma ta kasa ganewa. Babu tsammani suka yi kiciɓis da ɗan mama, ya kalleta ta kalle shi, ya ce "Ke! Me ki ke yi a nan wurin?" Ta ce "Yauwwa, kai ne wanda na gani a gidan Viper ranar ko?" "Ke, ki ka kuma kama sunansa, sai na ƙara wa ƙofar bakinki faɗi wallahi, kar ki sake ambatar sunansa ko ki kama sunansa". Nabila ta ce "Tom, ba zan sake ba, dan Allah taimakona nake son ka yi, ganinsa nake son yi dan Allah" Ɗan mama ya ce "Ka ga wata mayyar kuma, baki ji kashedin da yayi miki ba kenan? Kin ɗauka da wasa yake yi da ya ce "Ya sake ganinki zai kashe ki, kin san waye Viper kuwa?" "Ba zai kashe ni ba, muhimmiyar magana nake son mu yi da shi, na san na yi muku laifi, ku yi haƙuri dan Allah, ka taimaka mini ka haɗani da shi dan Allah" Ɗan mama yayi mata wani irin mugun kallo ya ce "Ya aka yi ki ka san ba zai kashe ki ba?" "Viper ba ya kashe mutane, mussaman mata da ƙanan yara, dan Allah ka haɗa ni da shi na kasa gane gidan". "Ke bar nan wurin, na haɗaku ki saka a kama shi ko, to ta Allah ba taki ba, wuce ki bar wurin nan" Ta sake marairaicewa za ta yi magana. Ya zaro wuƙa ya ce "Idan shi ba ya kisa ni ina yi, ware ko na zaro hanjinki yanzun nan" wuƙar sai ƙyalli take yi, ya fara tunkarota, yana wulwula wuƙar, ba shiri ta juya, gwiwa a sanyaye ta bar wurin. Har ta miƙe ta ɓacewa ganin Al'amin yana hangota, ya miƙe ya kwanta a kan dutsen, ya lumshe idanunsa rana tana dukansa, yana jin yadda zafin ranar ke ratsa shi, yana ƙara masa ciwon kai, amma ba shi da niyyar tashi. *** "P.A" "Na'am honorable" "Ka tabattar binciken da ka yi a kan yarinyar nan daidai ne, babu kuskure a cikin sa?". P.A ya jinjina kai ya ce "Babu fa, ka san ba na yadda a samu kuskure a irin wannan lamarin, mussaman a irin wannan ƙadamin, ba a samu kuskure ba, yadda na gaya maka hakan ne" Ya jinjina kai ya ce "Shikenan, ina ita ƙawar ta ta, ana cigaba da bibiyarta?" "Eh, a wurinta muka samu wasu abubuwan ma" Indabo ya ce "Haryanzu ina mamakin yadda aka yi ta ce ayi mata bincike a kaina ne, shiyasa nake ta tantama anya ka yi binciken a kanta dai-dai?" P.A ya ce "Haba honorable, ya ma za ayi wannan ƙaramar alhakin ta yi wani bincike a kanka, wataƙila hakan yana da alaƙa da harkar siyasa ne kawai, ko kuma sakata aka yi". "Ba ita ce a gabana ba, Viper mai zamani, shi ne babbar barazanata, shi ne damuwata, ku cigaba da aikinku kawai, duk abun da ake ciki, ka din ga sanar da ni " P.A ya ce "In sha Allah, ai yaronsa ɗaya yana hannu, sai dai na bincika an ce Haryanzu bai yi magana ya faɗi in da yake ba" Indabo ya ce "Ƙyale 'yan sandan nan, sonake na riga su samunsa, idan na riga su kawai kashe shi za ayi salin alin, duk madaki ne yayi mini shirme wallahi, amma yanzun ma komai zai daidaita" "Kar ka damu honorable, ai kai maganin kowane shege ne a ƙasar nan, ba ma ɗan daba ba, zamu yi maganinsa, amma da alama kamar kana da maguatan ɓoye, da suke tallafa masa" "Na sani, amma yanzu duk ba wannan ba, a cigaba da abun da yakamata" P.A ya ce "To shikenan, na barka lafiya " Bayan fitarsa Indabo ya shiga cikin gidansa, ya tarar da Abdul a falo, tare da mahaifiyarsa. Ya kalli indabo ya ce "Welcome" "Thank you" ya zauna ya kalli Abdul ya ce "Dama nemanka nake yi". Abdul ya ce "To gani" "Ya maganarmu ta rannan?" "Daddy maganganun namu ai da yawa, wacce daga ciki?". "A'a, ka san wanda suka fi muhimmanci ai, mun daddale da jam'iyya, kai za a tsayar mataimakin gwamna, tun yanzu yakamata ka fara harkar campaign, da buga pastoci. Amma ka san dole ka daina duk wani shashanci da kake aikatawa. Sannan maganar da nake yi, maganar aure, shekara talatin da biyar, uban me ka ke jira? Muddin lokaci ya cigaba da gabatowa, abokan adawa suka san baka da aure, sai ku samu matsala a harkar takarar nan, amma da na yi maganar auren sai ka din ga gocewa" Ya ɗan tsuke fuska ya ce "Wai constitution ne ya ce dole sai mutum yayi aure zai yi shugabanci meye amfanin auren mutum a cikin siyasa to?" Indabo ya ce "Ban sani ba, idan ba zaka yi ba, ni ina da wadda zan haɗaka aure da ita, ga 'ya'yan abokai da yan uwa nan sai  dai ka ji an yi". Hajiya Bilki da tun ɗazu ba ta yi magana ba sai yanzu ta ce "Haba distinguish, ka bi shi a hankali mana, zai yi, ba sai an yi masa dole ba". "Ba zan bishi a hankalin ba, na gaji da wannan shirmen nasa, rayuwarku nake ƙoƙarin ingantawa, wataƙila idan ya zama mataimakin gwamna, shi ya fi ni samun dama, ya kuɓutar da ɗan uwansa". Hajiya Bilki ta ce "Distinguish, kai da ka fishi daɗewa a harkar, ba ka samu yin hakan ba sai shi, ni na karaya da lamarin jafar" "No, kar ki yi mamaki ya fi ni samun authority, da damar fitar da shi, da dai a nan Nigeria ne, da tuni an daɗe da wuce wurin" Ta ce "Haka ne, Abdul dole ka yi haƙuri ayi maganar auren nan, tun yanzu za a fara share fagen samun damar yin nasarar ka, dan idan ku ka gama tenure ku, kai zaka yi gwaman nan gaba" Cikin sangarta ya ce "Mummy ba ƙi na yi ba, auren ne ba na so" "Aikuwa haka zaka yi haƙuri" suka cigaba da tattaunawa a kan yadda tsare-tsaren za su kasance. *** DSP Nasir na tsaka da aiki, aka sanar da shi yayi baƙuwa, ya ce ace ta shiga, tana shiga ya ga Nabila. Yayi murmushi ya ce "Ke ce baƙuwar dama?". "Eh mana, ko na koma ba ka san ganina?" "A'a ni na isa na na ce haka. Zauna bari na kawo miki lemo, daga wurin aiki ko daga ina?" Nabila ta kashingiɗa ta ce "Na je wani trial ne" Ya ɗaukko mata ruwa a fridge ya ce "Sannu" Ta ce "Yauwwa" ta karɓi ruwan ta sha,  ya ce "Amma kin bawa kanki wahala da yawa, wace court ɗin ki ka je, har ki ka iya biyowa nan?" Ta ajiye robar ruwan ta ce "Wani wuri na je, na ga wani client, DSP" "Na'am barrister Nabila maitama " Tayi murmushi ta ce "Wai ina mutumin nan?" Ya ce "Wanne?" "Wanda ku ka kama, haryanzu bai faɗi in da Vipern yake ba?" "Ina fa zai faɗa, yana ta wahalar da mu". "Dan Allah ka nuna mini shi" "Ki yi masa me?" "Babu komai, ganinsa kawai zan yi" Nasir ya ce "To bari na gama aikina, sai mu je ki ganshi" Nabila ta zauna ta jira Nasir ya gama abun da yake yi, ta ɗauki jarkar ruwanta suka fito, yana ta nuna wa abokan aikinsa ita, yana gaya musu ita yana gaya musu ƙanwarsa ce, lawyer ce. Suka gaggaisa da abokan aikinsa, sannan suka ƙarasa in da liti yake. Laɓensa duk ya bushe, saboda yunwa da ƙishirwa, yana ganin Nabila ya ganeta ya ƙura mata ido, ta kawar da kanta ta ce "DSP tun da ya ce bai san in da yake ba, haka zaku cigaba da ajiye shi?" "Eh har sai ya yi magana tukuna" Ta girgiza kai ta ce "Amma a doka, ai kotu za a kaishi ko a sake shi, ina ga fa tun da ya ce bai sani ba, bai sani ɗin ba" Nasir ya ce "Ya sani ba zai yi magana ba ne" ta miƙa wa liti ruwan hannunta, ta ce "Ga ruwa" banza yayi mata, Nasir ya juya ya fita yana amsa waya daga wurin ogansa. Tayi ƙasa da murya ta ce "Na san na yi muku laifi, amma dan Allah ka yi haƙuri, zan san yadda zan yi ka bar wurin nan". Ta ciro wani ruwan a jakarta ta bashi, ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri, na fahimci kuskuren da na yi, ban kyauta ba amma zan gyara komai" Nasir ya dawo ya ce "Mu tafi?" "Eh, amma gaskiya, yakamata a san abun yi, kar a taka doka da yawa" Ya ce "To masu doka, mu je gida" "Da gaske fa nake, ko mu shigar da hukumarku ƙara". Ya mayar da abun wasa, suka tafi gida. *** Ƙarfe huɗu na yamma, Nabila ta shirya ta fita, ta tafi gidan matar da aka ce an yi laifin fyaɗen nan a gidanta. Ganin Nabila cikin shiga mai kyau, ya sanya masu gadin ba su tsaya tuhumar wacece ba, suka bata damar shiga gidan. Sai da haushi ya fara kamata, saboda jiran da aka bar ta tana yi, daga baya matar gidan ta fito, suka gaisa da Nabila. Nabila ta ce "Na san baki sanni ba, sunana barrister Nabila Yusuf maitama, lawyer ce ni mai zaman kaina. Akwai mai gadin gidan nan malam isyaku, da ake accusing da laifin fyaɗe, ni ce lawyer sa. Na zo ne dan Allah in ji details ɗin abun da ya faru". Matar ta tsuke fuska ta ce "Ke, ni ki ka zo ki yi wa wannan tambayar? Wurin 'yan sandan na je na fara karɓar report, an ce na dawo station ɗin da aka fara case ɗin, amma na ga dacewar fara zuwa gidan nan, tun da an ce yarinyar 'yar aikinki ce, kuma ainihin wanda ya yi laifin kina da alaƙa da shi, ku ka yi framing ɗin sa aka ce shi ne. Yanzu duk ba wannan ba a matsayinki na uwa kuma 'ya mace nake so mu fara magana. Ina yarinyar take? Ina ne gidan iyayenta? Ban damu da sanin koma waye yayi laifin ba, fatana kawai a wanke mai gadi, tun da kun san wanda yayi laifin " Matar ta miƙe ta ce "Ki koma wurin jami'an tsaro, su zaki yi wa wannan tambayar, kuma ba ki da wata hujja, da take tabattar da ba shi yayi ba, idan kin gama kina iya tafiya" Nabila ta miƙe tsaye ta yi murmushi ta ce "Na gode sosai antyna da bani lokacinki" ta juya ta fice. Station ta sake nufa, wanda a nan aka fara case ɗin, aka nemo statement ɗin da aka rubuta, da sunan Asibitin da aka kai ramma, na cikin gari, tana tsaka da dubawa, wanda yake evening duty, shugaba a wurin, ya fito afujajan, ya ƙwace file ɗin wai ba a ba su damar su bata file ɗin tayi bincike ba. Cikin mamaki da takaici Nabila ta ce "Waye zai bayar da damar, bayan wadda ƙasa ta bayar, lawyer ce fa ni, dan me za a hana ni damar dubawa, doka ta bani damar neman hujjojin da zan gabatarwa kotu, na wanda zan kare, yaya za ayi a hana ni" Fafur suka hanata, suka ce ta tafi, ta kira Nasir a waya, amma wayarsa ta ƙi shiga, ranta yayi mummunan ɓaci. A gajiye ta koma gida, ana ta kiraye-kirayen sallar magariba, ta yi wanka tayi salla, ta ɗaukko wayarta ta kira sumayya. "Ke ya ki ke aikin?" "Sumy raina a ɓace yake, kin san menene?" Sumayya ta yi sauri ta katse wayarta, ta saka a Flight mode, ta ɗauki wayar ummanta, ta kira Nabila ta ce "Sorry wayar ce caji ya ƙare" Nan ta labartawa Sumayya abun da yake faruwa. Sumayya ta ce "In dai ƙasar nan ce, ai kaɗan ki ka gani d..... Cikin sauri Nabila ta katseta ta ce "Sumayya few months back, ina wannan case ɗin da yaya murtala ya saka, har aka kusa korarsa? The case are similar". Sumayya ta ce "How?" "In so many ways, dan Allah ki sake binciko mini labarin, ko ma ki haɗani da yaya murtalan, ke zan ma zo na same shi, the same yadda matar ta ce an yi wa yarinyar fyaɗe, ɗan yayan matar gidan, shi ma dattijon nan haka ya ce mini, ɗan yar matar gidan ne yayi abun ba shi ba ne ba, shi asibiti kawai suka kaita, da shi da ɗaya mai aikin da wani mai yi musu hidima a gidan, definitely duk case ɗin ne but i want to confirm" Sumayya ta numfasa ta ce "Ban ƙi ta taki ba, amma ki bi a hankali, kin ga a kan case ɗin, sai da Murtala ya kusa rasa aikinsa, ke daga ji kin san case ɗin babba ne" "Sumayya tsoron da muke ji, da ja da baya shi ke saka wasu ma suke Fuskantar irin matsalolin, idan na gama bincike na, i will raise the case, hatta 'yan sandan nan da abun da suka yi mini, duk sai na yaɗa, just support me sumy, Allah zai taimekemu, ke 'yar jarida ce, zaki iya kema". Sumayya ta ce "Haka ne, amma kar ki kira ni a wayata, zan ki ra ki da wani layin, sai mu haɗu da yaya murtalan" ta yi wa sumayya godiya, tana sake bawa kanta ƙwarin gwiwar lallai za ta tsaya wa wannan dattijon kuma za ta yi nasara. *** Abdul ne yake kallon ramma, yadda duk take a takure, tana kallon tv, amma hankalinta ba a kan tv yake ba. "Rahama" "Na'am" ta amsa tana kallonsa. "Meyake damunki ne?" Tayi shiru ta sunkuyar da kai. Ya kwanta a kan cinyarta, ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yana danna remote. Ya tashi ya ce canzo hijjabinki ki zo, ta yinƙura jikinta na rawa, ta sako hijjabi, ta fito. Ta tarar da shi a tsaye da mukulli a hannunsa yana waya. Ta ƙaraso jikinta yana tsuma, tunaninta ko gida zai mayar da ita, ya riƙe hannunta, ya buɗe ƙofar falon suka fito. Da kansa ya sakata a mota, ya rufe sannan ya zagaya ya kunna motar ya fita da ita. Sai kallon gari take yi, duk da dare ne ko ina da hasken fitila, tun da ya kawota a sume, ba ta sake fita ba, kuma ba ta san a ina take ba. "Gida zaka mayar da ni?" Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Ai na ce ki daina wannan tunanin ma" Cinema ya kaita, wai kallon film, bayan tv suka baro a gida, ta din ga waige-waigen yadda za ta yi ta gudu, amma a in da suke zaune, yana rungume da ita, ga wurin duk ƙabilu ne, abun da ta fuskanta, ba iya cinema ne wurin ba, dan daga can wani wuri, kaɗe-kaɗe na tashi. "Naga ki na ta waige-waige, ba mahaukaci bane ni, da zan kawo ki inda zaki iya guduwa, ko ki yi wa wani magana ba, kowa sabgar gabansa kawai yake yi a wurin nan, gara ma ki nutsu" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Ko bangon duniya zaka kai ni, idan Allah ya yi niyyar fitar da ni ba ka da dabara". Yayi murmushi kawai, sai da ya gama abun da yake yi, ya ɗauke ta, suka tafi ya kulleta a mota, ya sayo mata abinci, ya mayar da ita in da suke. *** Nabila kuwa tana ta bin kwatancen da dattijon nan yayi mata, na gidan zulai ɗaya mai aikin da suke aiki tare da ramma, amma ta kasa gane kwatancen, ganin ta gaji, kuma ta hanyar ake bi, a je in da Viper yake, ya sanya ta tare abun hawa, ta sake tafiya. A wannan karon da ta sauka, google map ɗin ta buɗe, tana duba abubuwan da suke wurin, ba tare da gazawa ba, ta cigaba da yawon bulayin neman gidan, cikin sa'a bayan shafe mintuna talatin tana bulayi, ta hango gidan. Wata irin ajiyar zuciya ta yi, sannan ta nufi gidan. Ƙofar gidan a rufe, ta saka hannu ta tura ƙofar, tayi sallama. Ƙofar ta buɗe, sai dai ba ta ji motsi ko alamar mutum a gidan ba. Duk da gabanta faɗuwa yake yi, amma haka ta ke ta addu'a ta shiga. Tsakar gidan ko ina shirgi, can bokiti, ga tukunya can kaya sauran sigari tsakar gidan kaca-kaca. Ta ƙarasa ta leƙa ɗakin, ta hango Viper durƙushe a kan gwiwarsa, yana ƙoƙarin yi wa kansa allura, sai dai hannunsa sai rawa yake yi, gashi ya huda jijiyar, jini ya fara zuba. Da sauri ta ƙarasa, ta durƙusa, ta gyara masa sirinjin, ta cigaba da zuba masa ruwan allurar. Rintse idanunsa yayi, jin yadda allurar take ratsa jikinsa. Babu tsammani, ta zare sirinjin ta ce "Wannan abun da ka ke yi, zai iya shafar ƙwaƙwalwarka fa" ba ta gama maganar ba, ta ji ya faɗo a jikinta, ta faɗi a wurin saboda nauyinsa, ƙoƙarin ture shi take yi, dan ji ta yi tamkar wani ƙaton dutse ne ya faɗo mata. Ya ɗago idanunsa ya kalleta, ya saka hannu ya shaƙe wuyanta. Numfashinta ya fara fita sama-sama, ta rirriƙe hannunsa idanunta suka yo waje. Walid ne ya faɗo ɗakin da gudu, ya fara ƙoƙarin janye Viper daga kanta. A tunaninsa jikin Viper yayi sakin da zai ture shi kawai, amma ya ji da ƙwarinsa. A wahale ta ce "Zaka kashe ni fa" a hankali ya saki wuyanta, Walid ya ɗago shi da ƙyar, ya kalli walid, ya kalleta ya sake mayar da idonsa kan Walid da ƙarfin gaske ya ce "Walid" "Na'am Al'amin" "Walid matata, matata walid! Ɗa na Walid mata ta" yayi maganar yana wani irin ƙaraji, tare da jan rigar walid da ƙarfin da sai da ta yage. "Easy maza, easy yi haƙuri" "Walid zan haukace, walid kaina zai tarwatse, me zan yi ne wai, ka fitar mini da yarinyar nan, ba na son ganinta matata walid" yayi maganar yana girgiza kansa. Nabila ta tashi da kyar, tana ta haki, ta ce "Zaunar da shi zan yi masa magana dan Allah" Walid ya ce "Ɗauki jakarki ki tafi, yi sauri" Kawai Viper ya shammaci Walid, ya buga kansa da ƙarfi a jikin bango, take jini ya fara biyo hancinsa, ya faɗi ya suma a wurin. Nabila ta ƙwala ihu, saboda sautin da kansa ya bayar, da ya buga kan, Walid ma a rikice ya ɗago shi, amma ko motsi baya yi. Ayshercool. 08081012143 49 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin matsanancin tashin hankali Nabila ta nufe su, Walid ya rikice, ya rasa me ma yakamata ya yi ya taimakawa Viper. Cikin azama Nabila, ta ɗaga kan Viper yana kallon sama, ta ciro hular kanta, ta toshe hancinsa da yake zubar da jini, ya zamana ta gefen bakinsa yake numfashi. Cikin kuka ta kalli  walid ta ce "A kai shi asibiti mana, ya bugu da yawa, tun da abun ya kai ga zubar da jini ta hancinsa" Walid ya ce "Ba za a kai shin ba, uban waye ya ce ki kuma zuwa ai duk ke ki ka ja?" Cikin rashin fahimta ta ce "Ni kuma? Ni me na yi? Zuwa na yi na bashi haƙuri a kan abun da na yi bisa kuskure, wallahi ban yi masa komai ba, tarar da shi na yi yana yi wa kansa allura jikinsa yana rawa, na karɓa amma wallahi ban yi masa komai ba. Ko duk haushin abun da na yi wa ɗan uwanku ne? Na je station ɗin ai, kuma na yi magana da shi, dan Allah ku yi haƙuri rashin sani ne ya sanya na aikata abun da na yi masa, abun da ake faɗa a gari a kansa daban, ni kuma ban san gaibu ba, amma dan Allah ku yi haƙuri" tayi maganar hawaye wani na bin wani a fuskarta. Walid ya ce "ya isa haka, tashi ki tafi" "A haka za a bar shi, ba zaka kai shi asibiti ba?" "Ta yaya zamu kaishi asibiti ana nemansa a kama shi?" Fizge-fizge Viper ya fara yi, yana ƙoƙarin tashi, Walid ya daddane shi, cikin ɗaga murya ya ce "Walid" Ya ce "Na'am Al'amin" "Liti" walid ya ce "Ya shiga banɗaki". Viper ya sake cewa "Mai laya" "Na kiyayi mai zamani, Allah ya ƙara maka lafiya" "Gobe zamu je asibiti da ƙanwarka 'yar madara, sun ce inducing za su yi mata 'yar madara za ta haihu, ragonta yana ƙauye wurin Hajiya" Walid ya ce "Masha Allah, Allah raba su lafiya" "Walid" "Na'am mai zamani" "Cikin nan yana ba ta wahala, nima na ƙagu ta haihu, na ga yarona, sunan ƙanina nura zan mayar, idan ta kuma haihuwa na saka sunan Sadik". Walid ya ce "To Allah ya kawo mana su lafiya da albarka" Wani irin ihu ya hau yi, yana ƙoƙarin ture Walid, cikin ƙaraji ya ce "Walid matata ɗa na, ba zan iya komai ba, ka riƙe madaki, kar ya illata mini mata, ka riƙe shi walid wai me ka ke yi ne?" Sosai suke kokowa da Walid, ga hancinsa na cigaba da zubar da jini, ga damuwa da fita hayyaci a dalilin allurar nan. Walid ya ce "Sai na ci uban ɗan mama idan ya dawo, bai ji me na gaya masa a kan kawo maka kayan maye ba, sai ya saka mun yi babu ka rasa ƙwaƙwalwarka tukuna". Nabila kuwa iya ƙarfinta take kuka, tsananin tausayinsa ya mamaye zuciyarta, da ƙyar walid ya danne shi, a hankali jikinsa ya saki, ya daina motsi, amma yana motsa idanunsa, a buge yake ya fita hayyacinsa amma ba bacci yake yi ba, abubuwan da suka wuce ne suke dawo masa cikin mayen. Nabila ta ce "Dan girman Allah ka gaya mini ƙarashen labarin nan, ina jauhar ina abun da yake cikinta?". Walid ya ce "Kin ga ni ba wannan ne a gabana ba, lafiyar ɗan uwana da taya shi ɗaukar fansa ita na saka a gaba, dan haka ki tashi ki tafi kawai" Nabila ba ta sake magana ba, ta tashi jiki a sanyaye, ta ɗauki jakarta, har ta kai bakin ƙofa, ta waiwayo ta sake kallonsa, hakan yayi dai-dai da buɗe idanunsa, sun yi jawur gwanin ban tsoro, ya tsura mata ido, a hankali ta juya ta fice. Cikin maye ya ce "Mai laya" "Allah ya taimaki mai zamani" "Ba na son ganin yarinyar nan, zan iya fara kisan kai a kanta". Walid ya girgiza kai ya ce "Ba ka taɓa yi ba, kuma ba zaka fara a kanta ba" surutan da Viper ya cigaba da yi ne, ya tabattar wa da Walid ba ya cikin hayyacinsa. *** Ramma ta na zaune, ta na cin farcenta, tana zancen zuci, ta ji Abdul ya kama hannunta. Sai da ta firgita, kasancewar tayi zurfi a zancen zuci. Hannunsa riƙe da nail cutter, ya fara cire mata faratan ya ce "Ƙazama kawai, da baki ki ke cin farce" janye hannunta ta yi ta ce "Ni kar ka shafa mini cuta" tayi maganar tana haɗe rai. "To cuta ta nawa kuma, in dai ina da ita da tuni kin ɗauka ta can wurin. Duk rashin ji na, ina using protection, a kanki ne kawai nake gaba gaɗi, shi ma dan na san am safe na killace ki" tsaki ta yi ta kawar da kanta gefe. Ya kama hannunta, ya cigaba da yanke mata farcen ta ce "A banza, wallhi ko haɗiyeni zaka yi, ka fito da ni, ba zan yafe maka zaluncin da ka yi mini ba" Bai kalleta ba ya ce "Dama ban ce ki yafe mini ba ai" ya na cikin yanke mata, ta ga yana ɗan yamutsa fuska, ya gama ya tashi ya koma ɗaki, ta kalli falon komai tsaf solomon yake gyarawa, a ranta ta ce "Dama aure ne da ni, ace nan gidana ne ba wannan ƙazantar ba. Tunanin hakan kawai ya saka idanunta cika da hawaye. Ta ɗaukko magazines ɗin da ke falon, tana ta kalla, har ta manta da shi a gidan, ta shiga bedroom ɗin, ta tarar shi a kan gado yana murƙususu. Ta kalleshi ta ce "Menene?" A wahale ya ce "Kira mini solomon" ta juya ta fita, ta kiro shi. Ya ɗaga kai ya ce masa ya kawo masa biro da takarda. Ya kawo masa, yayi rubutu a jiki, ya ce yaje ya sayo masa. Solomon ya fita cikin sauri, ta kalleshi ta ce "Wai menene?" Ya ce "Epigastric pain ne" "Me kenan" ya nuna mata cikin sa. Ramma ta ce "Sannu Allah ya sa mutuwa zaka yi na huta" Yayi mata shiru, ya cigaba da juyi, ya dunƙule hannunsa yana dukan gadon a hankali, yana yi yana miƙa alamar yana jin jiki sosai. Ta tsaya tana kallonsa, gumin da yake yi, ya sake tabattar mata ya fara galabaita. Yayi mata nuni da hannunsa ta je, ta ce "In zo in yi maka me?" Girgiza kai ya hau yi, yana kiran "Mummy, rahama cikina am in pain" "To sannu" Ta samo jarka da ruwa, ta tofa masa bisimillah ƙafa 19, da suratul fatiha ƙafa 7, ta hau kan gadon ta ce "To tashi ka sha ruwa" ya tashi da ƙyar ya karɓa, ya shanye, yayi jifa da jarkar, ya kwanta a kan cinyarta  ya ce "Rahama cikina" "Allah ne yayi maganinka, a cikin sakans idan ya ga dama, zai rabaka da rayuwarka, ka ga idan mutuwa zaka yi, ga saɓo kana yi, ga zaluncin da ka yi mini, Allah ya sa ka mutu". Abdul ya ce "Da na mutu shahidi, ciwon ciki ne ya kashe ni, kuma ƙarshe ace ke ki ka kashe ni". "Ko shahidi ka mutu kan ka shiga aljanna, sai ka shiga .... Sai kuma ta yi shiru. "Allah dai sai ya ƙwatar mini hakkina a wurinka na zalunta ta da ka yi" Solomon yayi knocking, Abdul ya ce ya shigo, ya shigo da leda a hannunsa, Abdul ya karɓa, ya sakawa kansa butterfly needle, ya saka ramma ta haɗa allurar da aka kawo, ya ce tai masa. "Ni ba zan iya ba, tsoro nake ji" "Tsoron me malama, ciwo zai kashe ni" "To ni taɓa yi na yi?" Cikin tsawa ya ce sai ta yi, hannunta na rawa, ta zuba allurar a cikin butterfly needle ɗin. A haka ya nuna mata yadda za ta saƙala masa ruwa, yana yi suna faɗa, ta saka masa ya sa hannu ɗaya ya janyota, ya sake kwanciya a kan cinyarta. Yadda yake wash wash da kiran sunanta, sai ya ƙular da ita kamar ba namiji ba. "Ni ka daina kiran sunana tun da ba ni na ɗora maka ba" "Wash rahama cikina" tsaki ta yi ta ce "Wai shekarunka nawa?" "36yrs" yayi maganar yana kallonta. "Amma an yi asarar ƙuruciya, idan ba ka yi wasa ba kana cikin wanda annabi ya ce kun yi asara, ka tafiyar da ƙuruciyarka a shirme da shashanci, a mintuna ashirin ɗin nan da Allah ya ga dama, da yanzu babu kai, me zaka ce wa Allah, ka sha giya ka kwana kana zina da 'yar da ka raba da uwatta, ka canza tunani da halaye, ko Allah ya yi maka rahama". Ya lumshe idanunsa ya yi shiru, bai ce mata komai ba. *** Nabila kanta tamkar zai tarwatse ita ma haka take ji, so take ta kamo bakin zaren tallafawa Viper. Babban abun da yake buƙata yanzu rehabilitation ne, a fara nesanta shi da shaye-shaye, sannan a kwantar masa da hankali da ƙoƙarin tirsasa masa karɓar ƙaddararsa ta hanyar da ya dace. Sannan a fuskanci kamo zaren tsaya masa, ya ɗauki fansar abun da aka yi masa ta hanyar doka, ba ta hanyar da yake tunanin ɗauka ba, sai dai alamu sun nuna mata ba zai sarrafu cikin sauƙi ba, balle a samu fahimtar juna da shi, sai dai ta ƙudurce a ranta, duk tsanani da wahalar lamarin, za ta tsaya a kan sa, ko da kuwa sanya rayuwarta cikin hatsari ne, za ta yi domin taimakon Viper. Sai dai hakan ba zata yiwu ba, sai ta ji ƙarshen labarinsa, amma ta yaya?. Da ta tuna yadda yake kururwa yana kiran matarsa, ɗansa sai ta ji ta karaya, tausayinsa ya ƙara kamata. Ringing ɗin wayarta ne ya katseta daga tunanin da take yi, ta ga lambar sumayya, ta ɗauki wayar ta kara a kunnenta. Sumayya ta ce "Na yi wa Uncle murtala kwatancen gidanku, zai zo ya same ki, sai ku yi magana". Nabila ta ce "Kai sumy, ban da ni ki bari na je na same shi, ni da nake nema?" Sumayya ta ce "Ya zo ya same ki is more safe, ba wanda zai kawo wani abu, kin san yanzu rayuwa babu tabbas mussman irin aikinmu". Nabila ta yi murmushi ta ce "Hakane masoyiyya, na gode sosai, saura ɗaya aikin" "Wanne kenan?" "Waye indabo?" "Kin ga ki raba kanki da indabon nan, wai me ki ke nema a kansa ne? Ba dai kin yi masa wulaƙanci kin ƙi gaishe shi ba, menene na bibiyarsa" Nabila ta yi murmushi ta ce "Ba zaki gane ba, ki taimaka kawai" "Nabila kamar kina ɓoye mini wani abu fa". "Ba abun da nake ɓoye miki, mamakinki kawai nake yi, duk kin canza kina abu kamar mara gaskiya kwanan nan sumayya" Dummm gaban Sumayya ya faɗi ta ce "Ban gane ba" Nabila ta yi dariya ta ce "Kar ki manta fa ni lawyer ce, idan na so zan gane idan ma baki da gaskiya, don't mind me kawai dai na ga kina ƙoƙarin kawar da maganar indabon nan ne, shiyasa nake tsokanarki, am about to do something big, zan gaya miki menene daga baya" "Nabila Please, kar ki je ki yi abun da ba shikenan ba, ki raba kanki da duk wani abu da zai sake haɗa ki da Aminu Vipern nan, kar ma a cetare ku ke. Ki bar DSP yayi aikinsa dan Allah" "Ni ba maganar Viper nake yi miki ba, case ɗin dattijon nan nake magana a kai, amma ki binciko mini maganar indabon nan, ko na binciko da kaina". Sumayya ta ce "To shikenan na ji zan yi, amma ki san in da zaki din ga zuwa da abun da zaki din ga yi kin ji arfan Abba" Nabila ta yi murmushi ta ce "Ji sai ka ce wata uwata, to na ji sai anjima" ta kashe wayar tana murmushi, a duniya bayan Abba ba ta tunanin akwai wanda ya kai Sumayya damuwa da ita, da tsoron ta aikata wani abu, da zai janyo mata matsala. Bayan sallar magariba, Murtala ya kirata a waya, ya sanar mata da ya zo, yana ƙofar gidan su. Ta saka hijjabi ta fita, suka gaisa ya ce "Sumayya ta ce "Ki na nemana" "Au ba ta yi maka bayani ba?" Murtala ya ce "Tayi mini, daga bakinki nake son ji". "Haka ne, ka ga wani case na samu, na wani dattijo, an yi framing ɗin sa, wai yayi wa wata yarinya 'yar aikin da yake gadi fyaɗe, na je na yi magana da shi, yayi mini bayani, ya ce ba shi bane ba, ɗan yayan matar gidan ne, so abubuwa da yawa are similar to rahoton da ka bayar kwanakin baya, shiyasa na ce bari na neme ka, ka ƙara yi mini bayanin yadda abun yake". Murtala ya numfasa ya ce "Kin san duk abun da aka ce, harka ta manya ce, sai dai a lallaɓa a yi komai a ɓoye ko ba haka ba, an ce yaron nan ɗan manya ne, kar mu je ki yi wani abun da zaki sakamu a matsala fa" Nabila ta ce "Uncle murtala, ba zan saka kowa a matsala ba, dattijon nan nake son na taimakawa, kunna mini recording ɗin matar, na sake ji". Ya kunna mata recording, ta saurara tiryan-tiryan, Nabila ta ce "Uncle murtala, case ɗin dai ai wannan, ba shi ne aka ce Naja'atu Bunkure ta shiga case ɗin ba, ai da na ce zan shiga case ɗin yarinyar". Ya ce "Shikenan, faɗuwa ta zo dai-dai da zama, amma dan zatin Allah don't mention my name". Ta jinjina kai ta ce "Kar ka damu in sha Allah ba zan yi mentioning ɗin ka ba. Naja'atu Bunkure ko da me take yawo a kanta, sai ta gaya mini in da case ɗin ya tsaya, ka san ina station ɗin da aka fara case ɗin, aka ƙwace file ɗin daga hannuna, wai ba zan duba ba". Haske su aka yi da fitilar mota, Nabila ta tura baki, tana kare fuskarta, Nasir ya gyara parking ɗin sa, ya fito ya nufo su. Ta ce "Yaya sannu da zuwa" bai amsa mata ba, ya kalli murtala ya ce "Malam ya dai, ya aka yi?" "Yaya idan saurayina ne, haka zaka yarfa ni dan Allah? Abokin aikin sumayya ne, muna tattaunawa ne a kan wani case". Nasir ya sake tsuke fuska ya ce "Kuma da daddaren nan?" "Eh, saboda shi ɓoyayyiyar shaida ne, da ba zan bayyana shi ba, ba na kuma son a samu trace, na wani ya ganshi, shikenan uncle murtala ka gaida gida" Yayi wa Nabila sallama ya tafi. Ta cigaba da yi wa Nasir mita, "Gaskiya yaya na fuskanci saboda kai wasu samarin namu suke tafiya, da haka za a aure mu, kana zare musu ido, kamar wasu 'yan ta'adda". "Eh, gara a zare musu idon, su san nan ba wurin da za su zo su kawo wargi bane ba" kawar da zancen ta yi, ta hanyar bashi labarin case ɗin dattijon nan, da yadda aka ƙwace file ɗin. Sosai ya din ga mita, har yayi alwashin rakata sake komawa station ɗin, a bashi tun da tana lawyer, dole a bata dukkan haɗin kan da take buƙata. Bayan ta koma ɗakinta, ta din ga murmushi itakaɗai, abu zai case zai haɗa ta da Naja'atu Bunkure, "Sai na ga abun da ya ture wa buzu naɗi kuwa" sai dai walwalarta ta ɗauke, bayan tuno wa da Viper, kar ta shagala da ramuwar gayya a kan Bunkure ta sakankance ta gaza samo mafita a kan nasa case ɗin. Tana buƙatar wanda zata tattauna case ɗin da shi matuƙa, amma ba ta ga wanda ya dace tayi maganar da shi ba. Dan ko da wasa ba zata tunkari DSP ba, balle sumayya tsfa zata ce za ta gaya wa Abba, dama ban da su biyun nan, ba ta wanda ya dace, ta sanarwa wannan gangancin da take shirin yi ba. Sai dai kwana ta yi, tana tunanin ko yaya Viper, ya farfaɗo gaba ɗaya ya warware ko kuma yaya? Washegari da safe, da DSP suka tafi station ɗin nan, a hanya yake sanar mata da an yi belin Liti, ta tambaye shi waye ya yi belin Litin, ya ce mata bai sani ba, waya kawai aka yi masa aka ba shi umarnin ya sake shi. Nabila ta ce "Nigeria ƙasata" Suka isa police station, Nasir ya nuna musu id card ɗin sa, sannan ya nemi su bashi file ɗin da Nabila ta nema, amma suka tabattar masa da an zo an karɓi file ɗin an mayar da shi babbar headquarter. Nabila ta ce "No wonder, hakan ya sake tabattar mini da lallai wanda ya aikata laifin, ɗan manya ne, kuma ba dattijon nan ne yayi ba" ta cewa Nasir kawai su tafi dama ta san a zaman farko sai an aike da baba prison, kafin ta gama tattara hujjojinta. Sai dai duk da haka, Nasir ya nemi a ba su in details, statement ɗin, da Asibitin da aka kai yarinyar, amma suka ce ba a ba su wannan umarnin ba, komai da komai yana babbar headquarter. Suna tafe take ce masa "Kar ka damu yaya, zan baka mamaki ƙoƙarin da zan yi a kan lamarin nan, zan tattara hujjojina na shiga kotu" yayi murmushi tare da ccigaba da ba ta ƙwarin gwiwa, ya biya ya ajiyeta a wurin aiki sannan ya tafi. Cak ta tsaya a harabar wurin, tana ƙarewa motocin kallo, ta tsayar da idonta a kan baƙin motocin da ta gani guda uku, sai dai ɗayar ita ce motar da ta din ga bin ta, har ta tsaya tayi knocking ɗin glass. Ta ƙarasa ta zagaye motar, ta sake tabattar da ita ce, ta jinjina kai ta shiga. Ta je office ɗin ta, ta ajiye jakarta, ta fita ta tafi office ɗin Barrister Habib, a hanya ta ci karo da MD barrister Kabir da wani babban mutum, da ta taɓa haɗuwa da shi a office ɗin sa. Cikin girmamawa ta risuna, ta gaishe su, suka amsa, Barrister kabir ya ce "'yar ƙwalisa in ji habib, an shigo kenan?" "Eh sir, na biya neman wata shaida ne, ban samu ba ma, na taho" Ya ce "Sai haƙuri, haka lamarin aikin dama yake, wataran nasara wataran sai haƙuri, na ji daɗi da na ga kina mayar da hankali yanzu kin rage kwalliya". Mutumin ya zuba mata ido, yana ta murmushi kamar an yi masa kyautar kujerar makka, dan sai da ta faki idon Barrister kabir, ta galla masa harara, sannan ta yi gaba. "Yaya Habib" Ya ce "Yau kuma?" Ta ce "Eh mana, yau baƙi muka yi ne? Ya gyaɗa kai ya ce "Dama wurin nan ai kullum cikin baƙi yake" "Wasu motoci na gani, wata farar mota ta waye?" Ya ƙura mata ido sannan ya ce "Hala na samu demotion ne zuwa mai gadi?" Tayi dariya ta ce "Am very sorry, ka san wani abu?" "Sai kin faɗa" "Ka san shi Allah, mai son bawansa ne, da kuma jin ƙan sa" Barrister Habib ya ce "Wannan haka yake". "A wannan karon, ba tare da na yi tsammani ba, akwai yiwuwar case ya haɗani da Najar bunkure, to kuma ka san ni yanzu kai ne mentor ɗina, na zo mu yi magana " Yayi dariya yana mayar da wasu files, drower gabansa ya ce "Nabila 'yar ƙwalisa, haryanzu ba ki san wacece Bunkure ba ko?" "And ba na buƙatar na sani, kawai i need your support, i want expose her hidden face to the world " "How?" Nan ta bashi labarin duk abun da yake faruwa, da case ɗin da yake hannunta. Ya ce "Nabila" "Na'am barrister yaya Habib" Yayi murmushi ya ce "Zaki ga yaya, aradu ki ke shirin tara da ka fa" "Na shirya mata". "Tana da wanda suka tsaya mata matar nan " "Ni ma Allah ya tsaya mini" Ya jinjina kai ya ce "Kin gama magana" Nabila ta ce "Yauwwa barrister, and i want you to support me, dan Allah ka taimaka mini" "Ba ƙi nayi ba Nabila, matar nan manyan mutane da manyan ma'aikata  sun kasa ja da ita, ke kin san ba haka nan take ba" Nabila ta sake gyara zamanta ta ce "Support me, you will be proud of me" Ya sauke numfashi ya ce "Duk abun da ki ke buƙata na taimako, ki yi mini magana kamar yadda na taimaka miki ki ga file ɗin Viper, zan cigaba da taimaka ki, amma ya zama sirri tsakanina da ke" tayi shiru tana kallonsa, ji tayi kamar ta yi masa zancen Vipern, sai dai a zuciyarta ta ji, ba ta gama amincewa da shi ba, kuma ba kowa za ta yi wa magana a kan case ɗin sa ba, dan haka ta yi murmushi ta ce "Na gode Allah ya saka da alkhairi ya raya maka zuriya. Amma yanzu ya kake ganin za ayi? Office ɗin ta zan je, a kan ina son bayanai daga gare ta, da bakin yarinyar?" "Eh mana, go as a barrister, ke ma lawyer ce, go with your full confidence" Tayi murmushi ta ce "Na gode sosai ranka ya daɗe" ta juya ta fita cikin farinciki. Sai dai kuma tunanin Viper ya cika mata zuciya, ko yaya jikinsa? Ya warware gaba ɗaya ko kuwa? Ba tare da dogon tunani ba, ta ɗau jaka ta fita, ta samu mai sayar da fruit, ta sai uban kayan marmari ta tari abun hawa ta tafi. Sai dai ta sha wahala, tana ta bulayi, ga uban kaya a hannunta, ta kunna Google map, yau sai ya fara yi mata hauka ta ce "Wai shi wannan ma anya ba aljani bane ba?" Har ta fitar da rai, kawai ta hango roofing gidan, haka ta cigaba da tafiya, har ta isa ƙofar gidan. Duk da tsoro da fargabar waccan shaƙar da ta sha, na neman kashe mata gwiwa, ta tsananta addu'a tare da neman kariyar Ubangiji. Jin sallamar mace ya sanya gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta, liti ya zabga ashar ya ce "Ke uban me ya kawo ki nan, munafuka macuciya?" Ta ce "Ashe kuma ka fito" "Ban sani ba, uban me ya kawo ki?" "Wurin Viper na zo" ta bashi amsa kai tsaye. Ya tashi tsaye zai zare wuƙa, Walid ya hana shi, ya ce mata "Me zaki yi masa, kin manta abun da yayi miki ne? Ki bar taƙama da baya kisan kai, zai iya farawa a kanki, dan yanzu ƙwaƙwalwarsa sai a hankali " Nabila ta ce "Shi ne dalilin sake zuwana, in ji ya jikinsa kuma na ji ƙarshen labarin nan" Walid ya ce "Jiki yayi sauƙi mun gode, amma ki tafi kar ki sake zuwar mana, saboda zuwan da ki ke yi zamu canza wuri" Liti ya fusata ya ce "Ke dalla fita" "Ka daina hantarata, ba wurinka na zo ba. Ni dai ku taimaka ku haɗani da shi, yakamata na ji da bakinsa ya yafe mink" "Ke! Ni ki ke gaya wa haka?" Walid ya ƙara dakatar da Liti ya ce "Ya riga ya yafe mikin ai" Ta girgiza kai ta ce "Ban ga alama ba, akwai buƙatar sama masa nutsuwar ƙwaƙwalwa kafin tunkarar duk wani abu, a ɗan zuwan da na yi, na fuskanci kuna amfani da ƙarfi wurin tursasa masa karɓar abun da ya zo masa a yadda yake. Baku da raunin, da zaku tausasa masa yadda yake buƙata" Walid ya ce "Kamar yaya?" "Kamar yadda nake faɗa yanzu, a fara samo ƙwaƙwalwarsa, ta hanyar daidaita gangar jikinsa, da hana shi ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, a saita tunaninsa da tunatar da shi shi wanene, ko ba duka ba, ayi ƙoƙarin samar masa da wani abu na farinciki ko yaya, a gwada canza masa tunani ba ta ƙarfin tsiya ba, kuma a sama masa likitan da zai din ga duba ƙwaƙwalwarsa" Walid ya ce "Taɓ, ke zaki iya duk wannan ɗin?" Cikin ƙwarin gwiwa Nabila ta ce "Ku bani dama, na san kuma a ba a karon farko ya karɓe ku ya saba da ku ba". Kafin wani ya kuma magana, ya turo ƙofa ya shigo. Walid ya ƙure shi da ido, dan kar yayi wa Nabila wani abu, ko nuna ya ga mutum a wurin bai yi ba, balle ya yi wani abu, ya shige ɗakinsa ya nemi wuri ya zauna a kan katifa. Babu fargabar komai, ta bi bayansa, tare da yin sallama a ɗakin, bai amsa ba kuma bai ɗago ba. Ta je gabansa, ta durƙusa da gwiwoyinta a ƙasa, ta ce "Ranka ya daɗe, wurinka na zo fa" ya cigaba da 'yan dube-dube. "Duk da na san, ba zaka amsa mini ba, amma na san kana ji na, wannan zuwan da na cigaba da yi, ina yi ne don neman afuwar kuskuren da na tafka bisa duhun kai, da rashin sani, amma dan Allah ka yafe mini ka yi haƙuri dan Allah" tayi maganar muryarta na rawa. "Dan Allah ka yi magana, wallahi na kasa sukuni, a dalilin jahiltal abun da ya sameka, ban san haka abun yake ba, ka yi magana ka ce ka yafe mini please" Still bai yi magana ba, sai dai ya ɗago ya kalleta, hakan ya sanya ta saurin cire idonta daga nasa. Ya miƙa mata hannunsa ya ce "Bani" Jakarta ta ɗaukko ta buɗe, ta ɗaukko wayarsa, ta miƙa masa, ya saka hannu ya karɓa, sannan ya ce "Sai da nayi kaffara a dalilin rantsuwa da na yi zan kashe ki, ban kashe ki ba, ki ka sake na sake rantsewa sai na aiwatar" "Da kuwa ka ci amanar 'yar madara" Ayshercool 08081012143 50 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin hanzari ya kalli Nabila, yana mamakin a ina ta san wannan sunan, dan sam bai san Walid ya gaya mata labarin sa ba. Ya ƙureta da ido, ta kawar da kanta gefe, ta ce "Eh, idan ka kashe ni, ka ci amanarta, ta barka ka kusa dawowa hanya, amma ka koma ruwa fiye da baya. Zan so na ji ƙarshen labarinta, amma kafin nan bari na tafi yanzu, ga kayan dubiya nan na kawo maka, Allah ya ƙara sauƙi" sai da ta gama maganar sannan ta ɗago ta kalleshi, still ita yake kallo. Ta sake cewa "Ina fatan zaka yafe mini laifin da nayi, rashin sani ne" ta tashi a hankali ta ɗauki jakarta ta fita, tana yi wa Allah godiya da wannan karon, ba ta sha shaƙa ba, hakan ya sa ta ƙara kin ƙwarin gwiwar cigaba da gwagwarmayar da ƙuduri aniya. Bayan fitar Nabila, Viper ya ɗaga kai yana kallonsu ɗaya bayan ɗaya, Walid ya ce "Ko ba ka yi magana ba, na san menene a ranka, ba kowa bane ba, ni ne nan na gaya mata labarinka". Ya tsayar da idonsa a kan Walid ya ce "Saboda me?" "Saboda dalili mai ƙarfi, cigaba da cusa kanta a lamuranka cikin duhun kai, tamkar ƙara yawan matsalolinka ne, zuciyar mace ta na da rauni, fiye da dukkaninmu, ina ganin hakan zai iya yi mana am..... Bai ƙarasa ba, viper ya katse shi ya ce "Ta yaya? Na ce ta yaya? Meye amfanin gaya matan, na gaya maka bana buƙatar cigaba da ganin yarinyar nan, sai an haɗa baki da ita an ƙara rusa ni kenan? Da raunin na su ake amfani a sarafasu a cuci mutum, halittu ne su marasa imani.... "Raunin 'ya mace, da tausayinta irin na halitta, kar ka manta shi ya jefa ka a cikin halin da ka ke ciki, idan mace ɗaya zuwa goma sun cutar da kai, ɗaya zuwa biyu sun yi maka abun da ba zaka taɓa iya biyansu ba, wanda tausayi da soyayyar da mace ta nuna maka, giɓin da ta bar maka ne, ya ƙara assasa tunzura zuciyarka ka ke fama da jinyar da muka rasa bakin zaren yi maka maganinta. Idan zaka yi adalci, ka yi musu hukunci da halin ƙanwata, Jauhar ko ba dukkansu ba. Yarinyar nan gaskiya ta gaya maka, idan ka yi kisan kai ka ci amanarta, wannan miyagun ƙwayoyin da ka ke ƙara ɗurawa kanka, su ma ba ka yi mata adalci ba". Al'amin da ya ji maganganun Walid sun ishe shi, sai ya miƙe tsam ya sake ficewa. Walid ya yi wa Ɗan mama inkiya ya bi bayan sa ya ga ina zai yi. *** Ramma ce take dukan gefen fion da Abdul yake "Abdulyasar Abdul yasar" ya buɗe idonsa da kyar ya kalleta. "Ka tashi ka yi sallar asuba, gari yayi haske, sallar ma baka yi" ya ja tsaki ya sake juyawa. Ta sake cewa "Ka tashi gari fa yayi haske" "Kin san jiya da daddare fa ban yi bacci ba, ki ƙyaleni" Ramma ta ce "Haka ne kam, dama ba ka da lafiya, wataƙila a cikin baccin za a zare maka rai, ban sani ba ko kana da abun da zaka gaya wa Allah a kan rashin salla" kan ta rufe baki ya tashi zaune yana ƙifta ido. Ta girgiza kai ta ce "Kai yanzu baka shirya wa mutuwa ba, ka ke rashin mutunci? Allah sarki ɗan Adam abun tausayi" ji yayi jikinsa yayi mugun sanyi, kamar mutuwar ce ke tunkaro shi, ya je ya yi alwala, ya fito ya tarar tana gyara gadon da ya tashi. Wayarsa ce ta fara ringing, ya tashi da sauri, ya ɗauka, ya saka a kunnensa "Hello mummy" "Kana ina ne?" Ya ce "Ina gidana" "To zuwa anjima ka zo gida, zaka yi magana da babanka, shugaban jam'iyya ya ce ka je ka ga 'yar sa, ku daidaita kanku, ayi magana dan ba za su yadda a baka takara ba, baka da aure". "Haba mummy, aure kuma? Ni wai dole ne auren nan, a haƙura mana" "Ban gane a haƙura ba, waye zai yadda ka yi deputy governor ba ka da aure, lallai ka zo anjima ku yi magana dama yana cewa ni nake hure maka kunne" Abdul ya ce "Ba ni da lafiya fa" "Ka sha magani ka zo, ulcer ce?" Ya ce "Eh, kuma wallahi ina jin jiki, dan Allah ki bashi haƙuri zan zo ne" Cikin damuwa ta ce "Ko na turo a ɗaukko mini kai, ba na son ciwon cikin nan naka fa" Ya kashingiɗa ya ce "A'a, zan warware, idan na ji sauƙi zan zo, sai anjima zan ɗan kwanta" ya ajiye wayar. Tun da ya fara wayar, ramma ta ƙura masa ido har ya gama. Ta ce "Ka ga banbancin rayuwar mace da ta namiji ko? Kaga duk abun nan da ka ke yi, kai an samo maka mata ni mecece makomata?" Ya kalleta ya ce "Kishi ki ke yi ne?" "Allah ya rufa mini asiri, na rasa a kan wa zan yi kishi sai kai, ka wulaƙanta mini rayuwa ka cuce ni, kai ka yi aure ka tara iyali, ni kuma babu wanda zai kalleni, ka yi mini fyaɗe ka mayar da ni ƙaramar karuwa, har ciki na ɗauka duk ta ƙazamar hanya ka wulaƙanta rayuwata" Abdul ya zauna sosai ya ce "Ke ki ka fara wulaƙanta rayuwarki, da ku ka yi yinƙurin cewa zaku nemi hakkinku a kotu, alhalin ba zaku iya ja da ni ba" "Sannu tsohon azzalumi, dama mai kuɗi shikaɗai Allah ya ce ya ji daɗi a duniya? Yanzu duk wannan abun taƙamarka kana da kuɗi ni 'yar talakawa ce? In sha Allah sai Allah ya ƙasƙantaka da kai da masu goya maka baya, suka tsaya maka kake rashin mutunci. Na san akwai ire-irena da yawa yaran talakawa da kuka zalunta, Allah ya na kallonku. In sha Allah sai Allah ya nuna maka iyakarka tun a duniya Abdul yasar" Duk da ya ji zafin maganganunta amma sai cewa yayi "Ko wanda ya raɗa mini sunan nan, bai kai ki iya faɗar sunan ba Rahama, Abdul yassar" Kallonsa tayi tana kuka, haushin kanta yakamata da lokacin da yake waya, ba ta yi ihu a wayar ta ce a taimaka mata ba sace ta yayi. Yanzu ko wayarsa ta ɗauka ba zata iya operating ɗin ta ba, kuma ba ta da lambar wanda ta haddace balle ta kira. *** Abba yana zaune yana kallon labarai a Aljazeera, Nabila ta shiga da sallama, yana kashingiɗe, ya tashi zaune yana murmushi ya ce "Barrister, kin yi mini wuyar gani da yawa fa, kullum na dawo kina aiki, baki dawo ba aiki ya hana mini arfana sukuni" Tayi murmushi ta ce "Abba ni kaina ina kewarka, bana samun zama, yanzu na shiryu ai, ina aiki sosai da sosai, na san addu'a ka ke yi mini" Ya ce "Kullum Addu'ata a kanku take, mussaman ke arfana, Allah ya yi miki jagora a dukkan lamuranki". "Eh mu ma Allah ba zai tagayyara namu ba" Umma tayi maganar tana harar Nabila. Nabila ko a jikinta ta ce "Abba dan Allah abu na zo roƙonka" Ya ce "Ina jinki ƴar albarka" "Abba dan Allah mota nake so, wallahi wahala nake sha samun napep, ayi ta haɗani da maza, ga zirga-zirga na yi ta kashe kuɗin mota, kuma haryanzu ni ba na yi wa client ɗina charges mai yawa" Yayi dariya ya ce "Nawa ki ka tara?" Tayi shiru sannan ta ce "Ina da 400k" Ya kwashe da dariya ya ce "400k, sai dai a gyara miki tsohuwar honda ta" Cikin shagwaɓa ta ce "Haba Abba, big girl kamar ni, da tsohuwar mota, ka taimaka Please" "Babu komai, za a sai mota in sha Allah, amma da sharaɗi ba na son yawon babu gaira babu dalili, kuma ke zaki din ga zuba manki, ba zan sai mota na din ga cacar mai ba" Cikin takaici Umma ta ce "Major mu fa? Muna zaune zaka saya wa Arfa mota, wannan wane irin rashin adalci ne?" Ya kalleta ya ce "Da walida zan saya wa mota, ba zaki faɗi haka ba, ku fa da me? Ga mota nan ana kai ku unguwa a ciki, meye na kishi da 'yar cikinku? Ku daina haɗa kanku da ita, kun san abun da nake nufi". Arfa ta tashi ta ce "Abba sai da safe" ta juya zata fita, ta yi wa Umma gwalo, a ranta ta ce "Saura ma babar su DSP idan ta ji, sai dai ku mutu". Ta koma bedroom ɗin ta tana murna, ta ɗauki wayarta, Viper ya faɗo mata a rai. Lambarsa da ta saka a wayarta, ta lalubo, ta zubawa ido, murmushi ta yi, ta kira lambar ta saka a kunnenta. Yana zaune a kan katifa, yana ta shan sigari, zubawa lambar ido yayi, ya gaji ya ajiye wayar, ya cigaba da abun da yake gabansa. Ba ta gaji ba ta din ga kiransa babu ƙaƙƙautawa, har sai da ya hasala, ya ɗaga wayar, amma bai yi magana ba. "Har na kusa fushi sannan ka ɗaga, na san da 'yar madara ce, ko ba ta san mai lambar ba, zata ɗaga kuma za ta saurareni, haka zalika zata yafe mini laifin da na yi mata. Akwai abubuwan koyi sosai da sosai a rayuwar ta, da ya ci ace ko ba duka ba, ka yi koyi da wasu, ba ta wulaƙanta ɗan Adam da tana yi, da ba ta riƙe ka da amana da tausayawa ba. Ina sake roƙonka yafiya, da kuma fatan samun haɗin kanka, ka ƙarasa mini labarinka da kanka, ina sha'awar kasancewa wani ɓangare na labarin nan, mai ban tausayi da ratsa zuciya Viper, sai da safe" tun da ta fara maganar, ya sunkuyar da kai, ya saki sigarin da take hannunsa, ya sunkuyar da kai hannunsa yana rawa. Ta gama maganar ta katse wayar, amma ya kasa ajiye wayar. Sai da liti ya dafa shi ya ce "Maza yane?" Ya ɗago idanunsa ya kalli liti. "Kamar Muryar wannan shegiyar yarinyar na jiyo a wayar, duk Walid ne da wannan sheɗancin" Ya cigaba da ƙurawa Liti ido, babu abun da yake fata, banda ya zubar da hawaye ko na mintuna biyar ne, amma ko na sakan ɗaya ya kasa tsawon shekarun nan. Murya a sanyaye ya ce "Liti" "Na'am mai zamani". "Ina kewar jauhar sosai" Walid da da yayi musu shiru, dan ya lura daga Viper har liti haushin sa suke ji, amma maganar da Viper yayi yanzu ta sanya jikinsa ya yi sanyi, tausayin Viper ya ƙara kama shi. "Da yanzu yarona ya isa shiga makaranta, wataƙila ma ta kuma haifa mini wasu" Walid ya taso, ya dawo gaban Al'amin, ya riƙe hannunsa ya ce "Ka ƙara haƙuri mai zamani". "Zuwa yaushe? Ko na ɗauki fansa kamar yadda nake buri da fata, kashe kaina zan yi saboda ba ni da wata makoma, idan kuwa hakan ba zai samu ba, zan koma in da na fito na ƙarasa rayuwata". "Dan Allah maza ka daina irin wannan maganganun, kana karya mana zuciya wallahi " liti yayi maganar cikin damuwa. Viper ya girgiza kai ya ce "Ba zaka gane ba" Kawai ya gyara ya kwanta, gaba ɗaya suka kewaye shi suna kallonsa. Nabila kuwa kallon wayar ta cigaba da yi, ta ce "Allah ya bani nasara a kanka, ya bani ikon taimaka maka". Kira ne ya shigo wayarta, ta ɗaga ta saka a kunnenta, ta yi sallama. "Wa'alaikum Salam da 'yar ƙwalisa". "Wa ke magana?" Yayi murmushi ya ce "Bawan Allah ne" "To, ai kowa ma bawan Allah ne, wanne daga ciki?" Yayi gyaran murya ya ce "Wani case ne da ni, nake so a taimaka mini" Nabila ta yi hamma ta ce "Office zaka zo, ba ta waya ba" ta katse kiran, dan a zatonta irin samarin nan, ne masu kiran wayar mata anyhow, duk da Muryar wannan ba ta yaro ba ce. Wani nannauyan bacci, yayi awon gaba da ita wanda babu abun da take yi ban da mafarkin Viper, dan sai da ta kusa makara yau. Kwanaki uku da zuwanta wurin su Viper, ba ta sake zuwa ba, she's very busy, tana ta off and down na tattara hujjoji, duk da ana ta taɗiyeta, duk in da za ta bi ta samo shaida, sai a rufe, sai da aka aike da dattijon nan gidan kaso. Gashi sai tayi ta sintiri a hanata ganinsa. Kamar uba da ɗa haka Walid yake ta lallaɓa Viper ya ci abinci, sai dai ya cakala ya bari, ba ya cin abinci. Private numbrn nan da ake kiransa da ita ce, ta kira shi, wayar tana ta ringing liti ya ce "Maza ka ɗaga mana" "Me zan ce?" Walid ya ce "Ko ba ka da abun cewa, ka ɗaga kawai" Ganin ba shi da niyyar ɗagawar, ya sanya Walid ya ɗaga ya sakata a hansfree. "Aminu Viper, kwana biyu. Ashe ta dawo maka da wayar. Alamu sun nuna kwana biyu ka yi sanyi, Kodayake kai sai an sakankance ka ke ɓarna. Gargaɗi nake sake yi maka, ka nesanta yarinyar nan da ga gareka, za a iya cutar da kai ta hanyarta". "Ni nake da ikon yanke hukuncin abun da yake daidai da rayuwata, babu wanda ya isa ya juya mini rayuwa yadda nake so, ka cigaba da ɓuya ko ka bayyana kanka, zan yi abun da nake ganin shi ne dai-dai da rayuwata. Mutumin yayi murmushi ya ce "Aminu Viper, shikenan idan ka ƙi ji, ba zaka ƙi gani ba ai" "Babu abun da ban gani ba, dan haka na shirya ganin koma menene" ya katse wayar. Liti ya ce "Duk walid ne ya janyo komai, ni na san a rina, wannan yarinyar idonta kawai zaka kalla ka gane munafuka ce" Kallon da Viper yayi masa ne, ya sanya shi yin shiru, Walid yayi dariya ya ce "Ayi dai mu gani, za a gane waye mai gaskiya tsakanina da ku". Liti ya ce "Ba wata gaskiya da ka ke da ita, ka dakatar da mu daga making moves, wallahi mun kusa fita operation kwanan nan" "Ku fita yaƙi ma ba operation ba" Haka liti da Walid suka kusa yin faɗa. Tun ana gobe Nabila zata je wurin Naja'atu Bunkure, suke waya da sumayya, take bata ƙwarin gwiwa, a kan za ta iya, kar ta ji tsoro. Da safe sai da ta fara zuwa wurin aikinsu, ta samu barrister Habib, shi ma ya ƙara mata ƙwarin gwiwa, da yi mata fatan alkhairi. Cikin ƙasaita take fiya a farfajiyar office ɗin, har ta ƙarasa, mutane ta tarar jingim. Wanda galibin su mata ne, suna jiran shiga wurin Barrister Naja'atu Bunkure. Kai tsaye Nabila ta shiga wurin sakatariyarta, ta nuna mata ID card ɗin ta, nan da nan ta bawa Nabila wurin zama, na ciki na fitowa ta yi mata iso zuwa wurin Barrister Naja'atu. Tun a hanya take maimaita "la hula wala ƙuwwata illa billa". Har ta shiga wurin Bunkure. Tayi sallama, ba tare da ta ɗago ta kalli Nabila ba ta amsa mata, ta ƙarasa ta zauna ba tare da an yi mata umarnin hakan ba. Kayan jikin Nabila kawai ta kalla, ta fuskanci ba kalar gajiyayyun da suke zuwa wurinta bane ba. Ta gyara zaman gilashin fuskarta ta na kallon Nabila. "Sannu da aiki ma" Nabila tayi maganar tana murmushi. "Yauwwa sannu" Nabila ta ɗaga mata id card ɗin ta ta ce "I am barrister Nabila Yusuf maitama" Bunkure ta jinjina kai ta ce "You look familiar to me" Nabila ta jinjina kai ta ce "Na yi mamaki ma, da ki ka iya tuna kamar kin sanni, saboda na san jama'ar ne da yawa. Ni abun da ki ka yi mini ba zan taɓa mantawa ba har abada" Bunkure ta ce "Ohh really" "Yeah and i have a promise to fulfil, a dalilin abun da ki ka yi mini" Ta kashingiɗa da jikin kujerarta ta ce "That's very good, ina son mutane masu yarda da kansu, ba na buƙatar sanin me nayi miki, ko kuma wani alwashi ki ka yi ba, ga ki ga bunkure Allah ya ida nufi " Nabila ta ce "Na ji daɗi da ki ka ce Allah, dan kuwa shi ne gaba da komai, na gode sosai barrister" "Mentioned not" Nabila ta gyara zamanta ta ce "Yauwwa, ba komai ne ya kawo ni ba, na zo ne a kan wani case, duk da ba mu haɗu a court ba, an kai wanda nake depending prison, amma ban ganki a court ba sai wakilanki" Bunkure ta ƙarewa Nabila kallo, sannan ta ce "Wane case ki ke magana a kai?" "Yarinya da aka yi wa fyaɗe, ki ka ce kin tsaya mata, ni ce lawyer wanda ake ƙara, na je wurin 'yan sanda ana ta yi mini yawo da hankali, ina son doctors report, kuma ina son zan ga yarinyar zan yi magana da ita". Naja ta yi wa Nabila kallon baki da hankali sannan ta ce "Kin san a gaban wa ki ke?" "I am barrister Nabila, ba ruwana da a gaban wa nake, ina neman hujja ne da zan kare client ɗina" "Nawa suka baki, ki ka samu ƙwarin gwiwar yin wannan kasadar? Zan ninka miki, ki ajiye case ɗin, kafin ki kunyata a idon duniya " "Watch your words, it can be use against you a kotu, kin san me nake nufi, you are also a lawyer" "Who the hell are you?" Bunkure ta yi maganar tana tashi tsaye, Nabila ma ta tashi tana sake ɗaga mata id card ɗin ta "Sai da na fara gabatar miki da kaina, sannan na gaya miki meya kawo ni. Ko dai ki bani abun da nake buƙata kawai, ko kuma na fasawa duniya wacece ke?" "Ni ɗin? Yaushe ki ka yi grduating, da me ki ke taƙama ki ke jin karanki ya kai tsaikon da zaki tunkare ni kina gaya mini maganar da ki ka ga dama?" Nabila ta girgiza kai ta ce "Cikin dukkanin girmamawa ta seniority a aiki, nake faɗar duk abin da nake magana a kai. You were my mentor before, abun da ki ka yi mini ya tabattar mini you are green snake under green grass. Keep your eyes open, Barrister bunkure, zan iya baki mamaki a lokacin da baki zata ba. Zan cigaba da bibiyar case ɗin ramma, da ƙoƙarin wanke wanda nake karewa har sai na yi exposing ainihin gaskiya ko da kuwa ita ce ajalina" tun da ta yi face to face da ita, ta ji duk wata fargaba da tsoron da take ji sun kau. Ta ɗauki jakarta, ta fita daga office ɗin. Tsaki Bunkure ta yi ta daki tebur, ta ɗauki wayarta, ta danna ta kara a kunnenta. "Yauwwa barrister Kabir ya kake?" "Lafiya ƙalau manyan ƙasa ya aikin?" "Normal ne, wacece Nabila a ma'aikatanka?" Ya ce "Lafiya kuwa? Ya aka yi ki ka santa? "Wacece ita, a id card ɗin ta na ga a wurinka take aiki" Ya ce  "Barrister Nabila, a law firm ɗina take". "Ta zubawa kanta fetur a jiki, tana kuri, idan na ƙyatta ashana, ba ita ba har kai, zaka ƙone ƙurmus ka ja mata kunne, ɓera ba ya taka rawa a gaban mage, ko da kuwa tana kan gargara ne" Kabir ya ce "Subhanallah, me ta yi?" "Ka bincike ta, ba na bari ayi mini kuskure biyu, ko yinƙurin yi aka yi, ina daƙile duk wani abu da zai kawo mini cikas". Kabir ya ce "Na fahimta, ki yi haƙuri dan Allah zan yi magana da ita, zan kuma ja mata kunne" ta ajiye wayar tana tsaki. Cike da annashuwa ta fito daga wurin, tare da jin kanta tamkar ta yi facing ɗin babban abun tsoronta. Ta tsaya a gefen hanya, ta ciro wayarta, ta kira Viper, ya ɗaga sai dai bai yi magana ba. "Hello, ya jiki? Na san ba zaka yi magana ba, dama so nake na ji ya jikinka, na so zuwa na ganka amma rana tayi sosai, zan je wani wuri ne, ka kula da kanka sosai" ta katse wayar, ji yayi tamkar ya aikata wani uban zunubi, ya din ga bin wayar da kallo, yana tunanin yarinyar nan tana da hankali kuwa?. Gida ta tafi cikin matsanancin farinciki, duk da ba su kwasheta da daɗi ba ita da. Gida ta tafi ta yi wanka, ta ɗauki wayarta ta kira sumayya, amma line busy. Ta ajiye wayar ta kwanta tana bacci. *** Shiru shiru Abdul bai je kiran iyayensa ba, yana nan yana fama da kansa, kuma ya hana duk abokansa zuwar masa gida. Duk da Allah ya isa, da fatan mutuwa da ramma take yi masa, hakan ba ya hanata tausaya masa, idan ciwon ciki ya murɗe shi, har mamaki take yi da ya ce mata ulcer ce, dan ita ta ɗauka yunwa ce take kawo ulcer, yaran masu kuɗi ba sa yi. Da daddare yana kwance a kan gado, tana zaune a ƙasa tana karanta wani novel na turanci, da ta ɗauka a falonsa, duk da ba wani ganewa take yi ba, amma yana ɗebe mata kewa. Tana ji aka kira shi a waya, ya ce yana zuwa, ya tashi ya fita. Bayan ya fita, ta ɗaukko pillow, ta ajiye a ƙasa ta cigaba da karatunta. Hamma da take ta yi ba ƙaƙƙautawa ne ya sanya ta gane bacci take ji sosai, ta tashi za ta rufe ƙofar ɗakin, kasancewar ya bar key ɗin ta ciki, dan ciwon cikin nan da yake yi, ta samu sassauci daga akuyancinsa. Sai dai ta buɗe ƙofar falon ba ya nan, ta fito ta wuce kitchen, ta daɗe a kitchen, ta zubawa fridge ido, komai akwai na morewa rayuw a gidan, amma gaba ɗaya ba ta jin daɗinsu, saboda ƙazantacciyar rayuwar da take ciki. Ta sha ruwa mai sanyi, ta cika cikinta,  ta fito falo, sai dai abun da ta tarar ya sanya gabanta mummunan faɗuwa. Cikin hanzari ya ture Nina daga jikinsa, ya yi tsilli-tsilli da ido, yana kallon ramma. "Abdul wacece wannan?" "Amm maid ɗina ce, mai aikina ce". "Kamar yaya, ina solomon ɗin, shi zaman me yake yi? Me ka ke yi da mace a zaune a gidanka? Abdul kar ka raina mini hankali mana, karuwa ka ajiye Abdul?" "Kar ki sake ce mini karuwa, ni ba karuwa ba ce, ke ce karuwa amma shi ki tambaye shi yadda aka yi na zo gidan nan?" Ta yi tsaki za ta tafi. "Abdul ka yi mini magana wace banzar ce wannan?" Abdul ya miƙe ya ce "ya isa haka, ki je gida za mu yi magana " "Ban gane ba, ka gaya mini wacece wannan?" Bayan ramma ya bi da sauri, Nina ta biyo shi, amma yana shiga ɗakin, ya mayar da ƙofa ya rufe da key ta ciki. Ramma tuni ta kwanta wani abu mai zafi ya tsaya mata a rai. "Rahma, ki tashi mu yi magana dan Allah, zan yi miki bayani" tayi masa shiru ta ƙi motsawa. "Dan Allah ki tashi ki ji, zan yi miki bayani" Ramma ta waiwayo sosai ta kalleshi ta ce "Ba ni zaka yi wa bayani ba, Allah zaka yi wa bayanin abun da kake aikatawa ba tare da tsoronsa ba. Ni baƙincikina, muzanta rayuwata da ka yi ne da wulaƙanta ni. Ka yi zina da wasu, ko wankan janaba baka yi, ka zo ka kuma afka mini, wannan wace irin rayuwa ce, Abdul yasar ka gama da rayuwata, wallahi ko baka kashe ni, ina son kashe kaina na huta, dan dai kawai ina tunanin makomata ne, amma ka cuceni wallahi" tayi maganar hawaye na ta gangarowa ta gefen idonta. Hannu ya sa yana share mata hawayen, amma ya kasa ce mata komai. Ya numfasa ya ce "Kina ji na?" "Dalla ƙyale ni, ba abun da zan ji, ni ƙyanƙyamika ma nake ji, mazinaci ƙazami mara tsoron Allah" Duk da yadda maganganunta suka yi masa zafi, amma ya daure ya ce "Dan Allah Rahma ki daina kirana da mazinaci, kalmar nan na yi mini ciwo sosai. Wallahi tun a kanki ban sake zina ba, yanzu ba abun da ki ke tunani ba" Aikuwa kamar ya tunzura ta, ta tashi zaune ta ce "Ni abun da ka ke yi mini menene? Na faɗa na kuma" ta sauka daga kan gadon tana huci, cikin ɓacin rai. *** Naja'atu kuwa tana zaune a bakin gado, tana ta haɗa ƙwayoyi a cikin roba, ta na zuba ruwa a ciki, shiru ta yi tana tunanin maganganun da Nabila ta gaya mata, mamakin ƙarfin halin yarinyar take yi, yadda ake shakkarta da shakkar yin gaba da gaba da ita, ita wannan yarinyar zata yi wa cin mutunci haka. Me take nufi da za tayi exposing ɗin ta. Ta daki teburin gabanta ta ce "Wai ma wacece ita?" Ta yi wata ajiyar zuciya ta ɗaga kai, ta shanye ƙwayoyin cikin robar nan da ta narka. Nabila ce zaune tare da Nasir, tana bashi labarin yadda suka yi da Naja'atu Bunkure, yake ƙara ja mata kunne, a kan ta bi sha'anin matar nan a hankali, kar ta yi mata illa. Tayi murmushi ta ce "In sha Allah ni zan karya alkadarin matar nan" Ya ce "To, Allah ya sa" Ya amsa da "Amin, na ji an ce kin ce mota ki ke so?" Ta jinjina masa kai ta ce "Abba ya saya mini mota,kai kuma ka din ga zuba mini mai" tayi maganar cikin shagwaɓa. Kasa amsa mata yayi, sai bin ta da kallo da yake yi, yana murmushi. Ta ce "DSP ya ake ciki ne, da zancen binciken viper?" Ya numfasa ya ce "Ina ta cigaba da bincike, gashi ana cigaba da matsa mini a kan kama shi, abubuwan ma na rasa yadda zan yi, duk shaidar da na kama sai ta zille, ace in sake shi, na rasa wannan wane irin abu ne. Amma dai an kwatanta mini wani yaro, dealer ne na wiwi, wai shi ɗan mama, idan na kama shi, ba zan bari a san na kama shi ba, sai na dangana da kama Viper in sha Allah" gabanta yayi mummunan faɗuwa ta ce "To wai suwaye suke sakawa a saki shaidun naka?" Ya ce "Ban sani ba, daga sama kawai ake cewa na sake su". Ta jinjina kai ta ce "Kuma anya ba su san in da yake ba, raina maka hankali kawai suke yi ba?" DSP ya ce "To ko ma dai menene, zan ɓoye bincikena, sai na dangana da kama shi, na danƙa musu shi, su san yadda za su yi da shi. Ina nan mun samu bayanan lokutan da yake zuwa an tabattar mana da idan muka kama shi, zamu iya kama Viper " Kamar an mintsine ta ta miƙe, ta ce "Bari na koma ɗaki, zan yi wani uzuri" har da gudu ta haɗa, ta tafi ɗakinta, ta ɗauki wayarta ta din ga kiran Viper, amma yaƙi ɗagawa, tayi masa missed calls sun fi goma, amma ko ɗaya ya ƙi ɗagawa, ga yamma ta yi sosai, idan ta fita kan ta dawo magariba zata iya yi. Ayshercool 08081012143 51 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Kamar Nabila za ta yi hauka, tana kallon kiran Barrister Kabir yana shigowa wayarta, amma ta share, taƙi ɗagawa, ƙarshe ma rejecting kiran na sa ta din ga yi, taƙi ɗagawa babban burinta kawai Viper ya ɗaga wayarta, amma yaƙi ɗagawa. Kwana tayi cikin zullumi, da addu'a kar Allah ya bawa Nasir nasarar kama Ɗan mama, dan a labarin Viper ba ta ji yadda aka same shi ba, balle ta san ingancin kasancewar sa tare da shi, tare da tabbacin ba zai faɗi in da Viper yake ba, kodayeke ta san ba zasu taɓa janyo wanda zai cutar da su ba. *** Abdul ne zaune a gaban Indabo, sai zazzaga masa faɗa yake yi, ya haɗe rai yana ta muzurai. "Ina magana kana shan kunu, Abdul ko ka ƙi, ko ka so dole ka yi aure, idan ba haka ba, babu yadda za ayi a ɗauki takara a baka, na gaya maka dan ba zaka yi mini asarar wahalar da na yi shekaru ina yi ba, dole ka je ka gano yarinyar party chairman ku daidaita, ko baka santa ayi, idan ya so daga baya sai ka auro wadda ka ke so" Cikin damuwa ya ce "Daddy, ya za ayi ace na auri wadda ba na so, ni tun ban ganta ba, ba na sonta wallahi, a bar ni zan kawo wadda nake so ɗin" Indabo ya ce "Inaa lokaci kuma ya ƙure maka, arranged marriage ɗin nan, duk cikin manufa ce irin ta siyasa, dan haka dole ka yi haƙuri, ka je ku daidaita" Abdul ya yi shiru bai ce komai ba. Indabo ya ɗora da cewa "Sannan za'a fara haɗa structures a kowacce mazaɓa, tun yanzu za ku fara campaign kafin ƙaddamar da takararku" Indabo har ya gama maganganun sa, Abdul bai saki fuska ba, yayi ya gama ya tashi ya bar office ɗin. Yana fita P.A ya shigo, ya ce "Distinguish yaya dai nake jiyo muryarka tun daga waje?" Indabo yayi tsaki ya ce "Abdul mana, gaba ɗaya yaron nan ba shi da hankali, wai shi ba zai yi aure yanzu ba, so yake yayi mini asarar wannan uwar wahalar da na sha muka kawo wannan matakin" P.A yayi murmushi ya ce "Rabu da shi, mu cigaba da dukkan shirye-shirye da suka dace, kuma a cigaba da bin malamai, dan Abdul akwai taurin kai, a kan auren nan zai iya fasa takarar amma a cigaba da matsawa". Imdabo yayi tsaki ya ce "Yaya ake ciki? Ya batun yarinyar nan?" "Mu na nan muna bibiyarta, sai dai bakin zaren gano in da Viper yake ne aiki, balle ayi masa tarkon da ita. A binciken da nake yi, shi wannan ɗan sandan ya kama liti, kwanansa kusan huɗu a hannunsa, aka ce lallai ya sake shi" Indabo cikin damuwa ya ce "Waye ya ce a sake shi ɗin?" P.A ya girgiza kai ya ce "Ban sani ba, haryanzu babu trace na wanda yake taimaka masa, kuma Viper yana nan a cikin garin nan yana yawonsa, sai dai gaskiya ƙarƙashin kulawar wani yake duk abin da yake yi " "Kaii wai wannan wane irin abu ne? Hankalina kullum a tashe yake, ban san ta ina zai ɓullo mini ya ce zai ɗauki fansa ba, ka san ba zai taɓa barina ba, shi ma wancan banzan da duk laifinsa ne, ya kasa komai ya kasa kamo shi ya kasa gano in da yake, duk shi ya ɓata lamarin, da bai tabattar da Viper ya mutu ba tun a wancan lokacin, ina cikin tashin hankali". "Ka kwantar da hankalinka distinguish, Viper fa zai zo hannu, ko da me yake yawo, ka yi haƙuri in Allah ya yarda babu abun da zai faru sai alkhairi" yayi ajiyar zuciya ba dan ya gamsu da maganganun P.A ba. *** Daga wurin Indabo Abdul gidansa ya wuce, ya tarar da Ramma na ta uban bacci, motsinsa a ɗakin ne ya saka ta farka, ya kalleta ya ce "Baccin nan ba ya isarki ne?" Ta ɗaga masa gira alamar eh. "Ko ki na da ciki ne?" "Allah ya kiyaye, ya tsari mahaifata da ƙara ɗaukar ƙazantarka" Ya ce "Hmm, ki bari cika baki, ki bari ayi gwaji tukuna" Ramma ta ce "Ba abun da za a gwada" Lambar saif ya kira, ya ɗaga ya ce "Yeah" "Saif daddy ya ɓallo ruwa fa" Saif ya ce "Zancen auren dai?" "Shi fa, wai wata 'yar party chairman, ni tun ban ganta ba, ba na sonta wallahi dan kawai zan yi takara, sai na auri wata wadda ba na so, ya dage ya dage, kamar na gudu wallahi". "Kai fa ka fiye gaggawa, ka bi su a sannu tukuna, ka je ka ga yarinyar " Abdul ya ce "Ba ma wannan ba, Nina ta ga yarinyar nan a gidan nan, tana ta yi mini hauka, ga maganar auren nan idan ta ji, ban san haukan da za ta yi ba, ni gaba ɗaya na rasa abun yi ma". Saif ya ce "Lallai ma Abdul, ba ka mayar musu da yarinya ba, kai baka kasheta ba, ka bar ta to yaya zaka yi da ita?". "Mu haɗu in anjima a joint kawai" Saif ya ce "Shikenan, Allah ya kaimu anjiman" yana kashe wayar ramma ta kalleshi ta ce "Bariki babu riba, dama duk wata hanya idan ba ta Allah, ai ba mai ɓullewa ba ce ba your excellency, na ga ku duniyar kawai ku ka saka a gaba, lahira kuma kun bar mana mu talakawa mu nema. Allah ya bamu a can. Ni dai in an tashi, a taimakawa 'yan garinmu da hanya, a gyara mana babban asibitin garinmu, sai kuma makarantunmu, dan Allah kar a manta da mu" Yayi murmushi ya ce "Ki na yi mini rashin kunyar za ayi abun da ki ke so?" "To ba ma so, dama kuɗin haram bana halal ba" bai ji haushi ba, ya kwanta a jikinta, yana kashe mata murya, yana kiran sunanta. "Rahmaaaa" ture shi tayi a fusace  ta ce "Ni ka daina yi mini wannan abun 'yan iskan ba na so" "Her excellency rahammaaa" yayi maganar kamar mai shirin yin shagwaɓa. Wani uban takaici ya cika mata zuciya, ta kasa ture shi, sai ma cakulkuli da ya fara yi mata, ta dunƙule hannunta tana kai masa duka, amma ko a jikinsa, dariya ma yake yi, abun nata gwanin ban dariya. *** Tun da aka idar da sallar asuba, Nabila ba ta koma bacci ba, ta shirya, gari na yin haske, ta ɗauki jakarta ta fice daga gidan, fuskarta sanye da niƙabi. A hanya gari ya ƙarasa waye mata, ta tafi gidan su Viper. Duk da akwai tafiyar ƙafa sosai, daga titi zuwa gidan, amma yanzu idan tayi bulayin, tana iya gano gidan. Kasancewar wurin da nisa, gari yayi haske sosai ta isa gidan. Ta tarar da su suna ta shirin ɗora karin kumallo. Walid ya kalleta da mamaki ya ce "Lafiya?" Ɗan mama ya ce "Mun shiga uku, wannan akwai mayya wallahi, idan ba kama mu aka yi ba, hankalinta ba zai kwanta ba". Liti ya miƙe a fusace, ya ɗauki wuƙa a kan taga, ya ce "Ke ware dan kazakazanki, ko shi bai kashe ki ba sai na kashe ki ni, jarababbiya kai, uban me ki ke nema a wurinmu? Ke bayan haushinki da nake ji, har da wannan banzan saurayin naki ɗan sanda da ya din ga azabtar da ni, sai na yi masa ido ɗaya, ba zai bar aikin ɗan sanda ba sai da tabona". Walid ya ce "Meya dawo da ke kuma? Me ki ke nema?" Ta ce "Viper" "Me zai yi miki?" "Ina son ganinsa ne" "Yana cikin yanayi mara daɗi, ki yi haƙuri ki tafi kawai, ba zaki ji daɗin abun da zaki gani ba" Nabila ta ce "Komai munin abun zan gani, zan jure" "Kin ga, ba mutuncinki bane ba, kina 'ya mace, ki dinga sintiri a gidan nan, wurin mutane irinmu ma, yakamata ki daina zuwa" "Zan daina, idan na samu abun da nake so, ka ƙarasa mini labarin jauhar, ni lawyer ce, ina son ya ɗauki fansa ta hanyar da ta dace ne, kuma niyyar da nake da ita ta alkhairi ce, dan haka na san ba zaku cutar da ni ba" tayi maganar tana nuna wa Walid id card ɗin ta. Walid ya ce "Na san ke lawyer ce" Cikin mamaki ta ce "Ta yaya?" "A ina na saka aka ɗaukko mini ke?" Sai kuma tayi shiru tana kallonsa. "Baki isa na bari ki raɓi Viper ba, muddin ban san wacce ke ba. Hatta gidanku na sani". Tayi ajiyar zuciya ta ce "Nayi mamaki, dama jiya na kira Viper ya ƙi ɗagawa, wanda ya kama ka, ba saurayina bane ba, yayana ne. Kuma da shi nake taimakawa a kan neman Viper, yanzu haka ya tabbatar mini da yi wa wani ɗan mama tarko, ya ce idan ya kama shi, an ce zai samu Viper, sai dai ban san waye ɗan maman a cikinku ba" Walid ya ce "Wani tabbaci muke da shi, ba zaki cutar da mu ba, ko ki ci amanar mu ba, duba da yadda ki ke zambatar ɗan uwanki cikin aminci" Nabila ta jinjina kai ta ce "Haka ne, ni zan tsaya a tsakiya ne, na bi ɓangaren gaskiya, and no matter what, ina da ikon tsayawa duk wanda nake ra'ayin tsayawa. Amma dan Allah ku bari na ganshi na yi magana da shi. Walid ya ce "To" Liti ya ce "Ni fa ban yadda da yarinyar nan ba mai laya, ya ya za ayi ta ci amanar ɗan uwanta kuma, ta ce tana tare da mu?" Walid bai kula shi ba, ya buɗe mata ɗakin da Viper yake ciki, yana zaune daga shi sai gajeren wando, ko riga babu a jikinsa. Jiki a sanyaye ya ce "Maganar da ki ka faɗa gaskiya ce, ƙwaƙwalwar viper ta fara samun matsala, a dalilin damuwa da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, yana buƙatar ganin likita, amma tayaya? Ina tsoron mu fita da shi a samu matsala". Duk ganin ƙirarsa ta razanata, yana zaune, daga zaunen ma maye kawai yake yi, ga uban karan taba guntu-guntu a wurin. Kawai ta shiga ɗakin ta nufe shi kai tsaye. Walid ya ce "Ki daina gangancin tunkararsa yadda ki ka ga dama, ba ya cikin hayyacinsa fa" Nabila ba ta saurare shi ba, ta je gaban Viper ta durƙusa, ya ɗago ya kalleta ya ce "Ban ce ki daina zuwa ba?" "Ba zan iya ba ne, na fara jin abun da 'yar madara take ji, idan ta ganka a yanayi mara daɗi, yaya za ta ji idan ta tsinceka a yanayin da ya fi na baya muni?" Ya zuba wa Nabila ido, wanda hakan ya tilasta mata kawar da kanta daga kallonsa. Ta cigaba da cewa "Yakamata ka ƙarasa mini labarin jauhar, kar na je na sakankance, ta dawo ta ƙwace mijinta, dan a labarinta na ga daga tausayi soyayya ta ƙullu, kuma nima dai gashi ba na son shaye-shayen nan, kar na je sai na yi nisa ta ƙwace mini kai, tana ina ne yanzu?" Tayi maganar tana jiran amsar da zai ba ta. Ya ƙura mata ido, har sai da gabanta ya faɗi, ta fara tunanin ko shaƙetan zai yi. Amma ya jingina da bango yana lumshe ido. "Talk mana" tayi maganar da sigar rarrashi. Su liti duk suna window suna ganin ikon Allah, su ihu yake ta yi musu, yana kiran matarsa, amma yanzu ya nutsu, ko hargowar bai yi mata ba. "Na ga haryanzu baka gama dawowa dai-dai ba, bari na je zan dawo, sai mu yi magana ka din ga ɗaga wayata amma, sunana Nabila Yusuf maitama. Amma babanmu arfa yake ce mini, ranar arfa aka haife ni, shiyasa nake da sa'a sosai kuma yana son mamana sosai da sosai, kamar dai yadda ka ke son 'yar madara. Amma dan Allah ka gaya mini da wuri tana ina, kar in zo daga baya, ka ce baka san zance ba baka sanni ba". Tayi masa maganar cikin sigar shagwaɓa. Yayi shiru, ko tari bai yi ba. Har ta gama surutanta, bai yi magana ba, ta tashi a hankali ta fito, ta kalli Walid ta ce "Zan je gidan masu rangwamen hankali, na yi magana sa likitocin ƙwaƙwalwa, idan ta kama dole ayi arranging yadda zai ga likita, ina matuƙar buƙatar hankalinsa, kafin komai ya yiwu, sannan ku rage zirga-zirga an matsawa yayana lamba a kan kama shi, kuma ya dage by any means sai ya kama shi". Walid ya ce "Shikenan, mun gode da gudunmawarki, sai anjima" ya jinjina kai ta fice ta tafi. Suka sake leƙa Al'amin, ya kwanta a wurin, yayi ruf da ciki, wanda tun bayan sallar asuba suke fama da shi, sai ya fita ya kashe madaki da Indabo, da ƙyar suka rufe shi a ɗaki, da kokowa, dan kuwa sun sha wahala, duk da su uku ne, shikaɗai neman gagararsu yayi, amma da Nabila ta zo tana yi masa magana bai yi wannan hargagin ba. Sai kusan sha biyu saura ta isa wurin aikinsu, mai yi musu goge-goge ne ya sanar da ita, Barrister kabir yana ta nemanta, ta ce masa to, sai da ta shiga office ɗin ta, ta dafa tea a dispenser tana da biscuit a office ɗin ta, ta haɗa ta karya. Sai da ta kammala, sannan ta tafi office ɗin Barrister kabir, yana ta shiri zai fita yana da wani meeting, duk yadda yake yi mata wasa, idan suka haɗu yau sai ya sha kunu ya ɗaure fuska tamau. "Sir an ce kana nemana?" A ƙule ya ce "Au an ce nema? Tun jiya nake kiran wayarki, baki ɗaga ba, baki biyo ba ki ji dalilin kiran" Cikin ko in kula ta ce "Sir ban taɓa yin hakan ba, yakamata ayi mini afuwa ayi mini uzuri" "Shut up, ba zaki janyo mana magana ba, kin san wacece matar nan kuwa?" "But sir, this is my personal trial, ba under law firm ɗin nan zan yi shari'ar nan ba". "Ina magana kina magana? Amma da ID card ɗinmu ki ke amfani ko? You better watch what you are doing, faɗa da matar nan tamkar faɗa da manyan mutanen nan ne, dan su take yi wa aiki" Barrister Habib ne ya ƙaraso, yana faɗin "Subhanallah, lafiya kuwa meyake faruwa?" Barrister kabir ya ce "Ka san yarinyar nan office ɗin Naja'atu Bunkure ta je neman magana, wai tayi mata bayanin wani case da yake hannunta, ina ruwan Nabila da Bunkure?" Idanun Nabila ya cika da hawaye, tamkar ta fashe da kuka, kowa ya santa da barrister Kabir, suna good time sosai, amma yau yayi mata ihu a gaban mutane. Barrister Habib ya ce "Barrister Nabila, garin yaya, meyasa ba kya shawara waye ya aike ki? Kin san wacece Bunkure kuwa? Gaskiya kin yi wauta, mu je in ji ya aka yi, barrister yau da kai da daughter taka mu ganku a rana, amma ayi mana afuwa, ka san yanzu nine abun koyinta, mun shirya tana son aiki tana ƙoƙari. Ayi mata afuwa". Kabir ya girgiza kabir ya ce "Rigimarta tayi yawa" "Ayi haƙuri ke kuma wuce mu je" Barrister Habib ya sakata a gaba, suna zuwa Office ɗin sa, ta fashe da kuka. Ya ce "Ahhh ya haka? Kuka kuma karaya tun yanzu?" Cikin kuka ta ce "Kana ganin abun da yayi mini, ita wacece Naja'atun ba mutum ba ce ba? She's just my senior kuma ni ba rashin kunya na yi mata ba, ajiye masa aikinsa zan yi nayi zaman kaina" Barrister Habib ya yi dariya ya ce "Kin bani kunya, waye ya ce miki ana gwagwarmaya babu ƙalubale ne? Dole ki shiryawa ƙalubale, and ki bar maganar resigning ɗin nan ba mafita ba ce ba. Yanzu yaya ku ka yi da ita?" Cikin tura baki ta ce "Ni sai na bar wurin nan" "Kar ki ga laifinsa, maybe kiransa aka yi, aka ja masa kunne, dan haka ki yi masa uzuri ai bai taɓa yi miki haka ba ai, haba 'yar ƙwalisa". Ta zumɓura baki, tana goge hawayenta. "Yanzu yaya ku ka yi da ita?" Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Nothing much, alamu sun nuna babu gaskiya a lamarin nata, dan idan tana da gaskiya, zata gaya mini aka tsaya a lamarin yarinyar, amma ta kore ni, ta ɓuge da kiran sa. Sai dai an hana ni ganin shi wanda nake karewar ma, amma dai ya kwatanta mini gidan ɗaya mai aikin, na je an ce ta tashi ta koma garinsu. Amma ya tabattar mini da yarinyar 'yar tofa ce, wai wani gari yaloko, amma bai san ina ba a tofa. Ni ban san ina ne ma tofan ba, balle na nemi gidan su yarinyar". Barrister Habib ya yi shiru sannan ya ce "Kin tabattar a tofan ya ce miki take? A yalokon?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "To shikenan, ki bani kwanaki i will get back to you. Amma ki daina garaje, ki din ga bin komai a hankali" Ta ce "To" ya din ga rarrashinta, har ta huce, ta tashi ta koma office ɗin ta". *** Tun da Abdul ya dawo, yake cika yana batsewa, ramma ko kallo bai isheta ba, ta cigaba da sabgoginta, ko abinci bai ci ba, ya nemi wuri ya kwanta. Haushi ya ishe shi, gaba ɗaya ba ta tasa take yi ba, karatun littafinta ne kawai a gabanta, babu tsammani ta ji ya fizge littafin hannunta. Ta kalleshi ta ce "Lafiya?" "Wai ke wace iri ce ne?" Ta kalleshi ta ce "Kamar yaya?" "Ke baki damu da ki ga mutum cikin damuwa ba, ki tambayi meyafaru ba?" Ramma ta ce "To ina ruwana da abun da ya dameka? Ni banda damuwar da ka saka ni a ciki? Bani littafina malam". Abdul ya ƙura mata ido, ta tashi zaune ta miƙa masa hannu ta ce "Bani dan Allah". "Me ki ke ganewa a ciki ne?" Ramma ta ce "Ko ba na ganewa, ai gara na karanta littafin, da kallon fuskarka ma, bani littafina malam" ta yi maganar tana haɗe rai. Wayarsa da take vibrating ya ciro, ya saka a kunnensa. "Yau Yakamata ka shigo Asibiti, yau zaka yi wa patient ɗin ka tiyata fa" Ya ɓata fuska ya ce "Yau ne amma baku tuna mini ba, ni na manta gaba ɗaya". "An yi booking ɗin su, da wanda za su ganka, kusan wata biyu suna jira, ba su samu ganinka ba" "Zan kira Doctor Anas,ya je yayi am sick, ba zan iya tiyata ba" "Amma doctor... Cikin hargowa ya ce "Shut up, abun da na ce za ayi" "To shikenan" ya ajiye wayar, ramma ta ce "Dama kai likita ne?" "Ban sani ba, sai yanzu ki ga damar kula ni, saboda baki da imani, ki na kallo ko abinci na kasa ci". "Kar Allah ya sa ka ci mana, kai har ka na bakin cewa wani bashi da imani Abdul yasar? Hala tsabar imanin ne ya sa kazo ka yi mini kurkuku a nan?" "Ke fa taimakonki nayi, haka ki ka zo kalli yadda ki ka yi ƙiba, ki ka yi kyau, sai ma mun ci gwamnati, zaki fi haka ƙiba" yayi maganar yana taɓa damtsenta. "Ni meye nawa idan ma kun ci gwamantin, in sha Allah ma ba zaku ci ba, ace a rasa wanda za su jagoranci al'umma, sai mutanen banza masu lalata yaran mutane " ya ce "Ok, Ai ba a wurinki muke nema ba" "In sha Allah ba zaka ci ba, ko ƙuri'a ɗaya ba zaka samu ba" Abdul ya ce "Ke ki ka sani, na je na ga yarinyar da aka ce zan aura, kyakykyawa nutsatiyya, tabbatar Allah ba ya karɓar addu'arki" Da sauri ramma ta kalleshi ta ce "Nutsatiyya, ai ba zaka taɓa auren macen kirki ba, sai wadda wani ya lalata kamar yadda ka yi. Ai ko ka ganta a nutse ma, in sha Allah irinka ce zaka aura. Ba zan yi fatan Allah ya baka lalatacciyar 'ya ba, dan ba ita tayi mini ba, amma in sha Allah sai ka auri lalatacciya" tayi maganar tana hawaye. Abdul ya ce "A'a gaskiya ba lalatacciya kamar ke ba, Nutsatiyya ce sosai, idan na aureta kar ki damu, ba zamu rabu ba, ai ana mugun tare tun da kin zama 'yar hannu kema. Ta ce "Kai da Allah, kuma in sha Allah sauran wani zaka aura" Abdul ya ce "Nima saurana wani zai aura, balle ba zamu iya rabuwa da juna ba, mun riga mun saba, ni zan iya aure, amma ke ba zaki iya ba, kawai mu cigaba da rayuwarmu a haka rahma". Hawaye wani na bin wani ta ce "In sha Allah, sai Allah ya kuɓutar da ni daga hannunka azzalumi kawai" Abdul tamkar jin daɗin tsinuwar da ramma take yi masa yake ji, ta zage shi tayi masa Allah ya isa, amma hakan ko a jikinsa, sai ma cigaba da tunzurata da yake yi ya ce "Ohhh kishi a fili, ki dai yi a hankali, kar ki yi zurfi a soyayyata, 'yan mata ne da ni burjik" "Eh tun da ga ka bunsuru ba" ta tashi tsaye tana kuka. Ya ƙyaƙyace da dariya ya ce "Bunsuru ya ajiye akuya ta mussaman a gidansa ba" kalmar akuyar tayi mata ciwo, kawai ta fita daga ɗakin ta bar shi, yana ƙyaƙyata dariya. *** Indabo yana ta shiri zai koma Abuja, hutunsu na majalissa ya ƙare, ga shirye-shiryen da ake yi na fara zaɓen fidda gwani, wanda yake ta fafutuka a tabattar da yarjejeniyar da suka yi na ba wa Abdul takarar mataimakin gwamna. Sai dai sai fama yake da shi, idan yayi nan sai yayi can. Naja'atu Bunkure ce ta kira shi a waya, ta ce masa tana office ɗin sa na gidansa, tana son ganinsa. Ya san muddin ta yi masa zuwan gaggawa ba bu sanarwa, akwai damuwa ne, dan haka ya ajiye abun da yake yi, ya fita. Ya shiga ya zauna yana faɗin "Naja'atu masu ƙasa ya ake ciki ne?" Ta kalleshi ta ce "Ina Abdul?" "Oho masa, yana can tasa shiririta ya tattara ya koma gidansa da zama" "Akwai ƙura fa" Indabo ya ce "Wace irin ƙura kuma?" "Yaya yayi da yarinyar da ya yi wa fyaɗe?" Indabo ya ce "Mun yi magana da shi, ya ce mini ya kasheta" "Ka tabattar da hakan kuma? Akwai matsala fa. Wata shegiyar yarinya ta zo office ɗina, wai na bata bayanan in da aka tsaya da maganar yarinyar, wai zata tsayawa mai gadin nan, hankalina ya kasa kwanciya jikina yana bani, ba itakaɗai take wannan abun ba, akwai abun da ta taka, duk da na kira law firm ɗin su na yi musu warning, amma jikina yana bani akwai wata a ƙasa, kar ta zurafafa ta gano wani abu, dan yarinyar a tsaye take babu alamar kunya a tare da ita". Indabo ya ce "Kin daɗe kina magance matsaloli da rigingimun da Abdul yake ɗaukkowa, amma ya aka yi na ga karaya a tare da ke yau?" "Ba karaya nayi ba, ka san hausawa sun ce, rana dubu ta ɓarawo, ɗaya tak ta mai kaya, na so ƙarasa aikin da kaina, amma ka ce na bari zai yi maganin abun, ka nemo ɗanka ka tabattar da bai bar wani trace ba, gobe in Allah ya kaimu zan tafi conference ɗin da shugaban ƙasa ya tura mu, dan haka ba zan samu damar zuwa gidan su yarinyar ba, dan haka ka nemo shi" Indabo ya ce "Naja'atu, idan aka samu matsala the blame will be on you, sakacinki ne" Naja ta girgiza kai ta ce "Sakacinku dai, na yi iya yi na ni, yadda ku ka yi da shi, ka sanar da ni" Indabo cikin hanzari, ya ɗauki wayarsa yana kiran Abdul, sai dai wayar taƙi shiga gaba ɗaya. Nabila har wata ramar dole tayi, saboda zirga-zirga, gashi kwana biyu ba ta je wurin Viper ba, gashi tana cikin damuwa da tsananin son ganinsa. Gaba ɗaya yanzu ba ta doguwar shawara, kafin ta tafi gidan Viper, yau ma haka babu tsammani sai ganinta suka yi rana tsaka. Duk suka bi ta da kallo, ta kalli Walid ta ce "Ina wuni" "Lafiya ƙalau" "Ya mutumina, ina fatan yana lafiya?" Walid ya ce "To da sauƙi dai, yana ciki" Liti ya ce "Wallahi ba zata shiga ba, ke ware, ni fa ban yarda da yarinyar nan ba". Nabila ta kalli liti ta ce "Ka kiyaye ni fa, ba ruwanka da ni, ba wurinka na zo ba, wurin Viper na zo, zan duba lafiyar sa kuma mu yi magana" Walid ya ce "Dan Allah liti ka daina haka, mana wai me ta yi maka ne, ta bayar da haƙurin abun da tayi ai" Liti ya ce "Ni fa ba a iya yaudarata cikin sauƙi, fita malama, ba zaki ganshi ba" "Ba zan tafi ba sai na ganshi, ba ruwanka da ni". Ya zazzaro mata ido zai yi magana, ya ji an hankaɗe shi daga bakin ƙofa, Viper ya fito yana ƙanƙance idanunsa. Suna haɗa ido, ta sakar masa murmushi, mai cike da nuna farincikin ganinsa, duk kallon na sa tsoro yake bata. Liti ya ce "Mai zamani mai hakan yake nufi? Kai ma ka yarda da wannan munafukar, ita fa ta saka aka kama maka ni, aka rufe ni so take sai an kama ka fa". Walid ya ce "Kai ɗin uwar me ka ke tsinana masa?" Duk bai kula su ba, ya taka ya fito ya ɗauki brush da toothpaste, ya matsa. "Ina kwana" tayi maganar tana bin bayansa. Bai amsa ba, ya durƙusa yana wanke bakinsa. Wayarta da take ta vibrating ta ciro, ta saka a kunnenta ta ce "Hello" "Ke Sumayya ce" "Ohh sumy, kullum cikin sauya lamba kamar 'yar yahoo?" "Malama kwana nawa ina nemanki a waya ban same ki ba, kuma baki neme ni ba" Nabila ta ce "Sorry na yi laifi" Sumayya ta ce "Yaya ku ka yi da Naja'atu baki gaya mini ba" Nabila ta ce "Ke zan zo gida na baki labari, ina wani abun ne yanzu, dan na kusa rubuta resigning na ajiye musu tsiyar su, na fuskanci Naja'atu Bunkure gaba da gaba, naga gani take ita wata jan wuya ce, ko ban kaita ƙasa ba sai na razanata" gaba ɗaya suka zuba wa Nabila ido, cikin hanzari Viper ya ɗago ya zubawa Nabila ido, ta katse wayar ta ce "Meyafaru ku ke kallona ne?" "Naja'atu Bunkure" ya maimaita yana kallon idon Nabila. Cikin rawar baki, saboda tsorata da kallon da yake yi mata ta ce "Ka santa ne?" "Mu je waje mu yi magana" Ayshercool 08081012143 52 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Jikinta ne ya hau tsuma, saboda irin kallon da yake yi mata, yayi gaba da nufin ta bi bayan shi, amma ta ƙi, ya tsaya ya waiwayo yana kallonta, ta kalli Walid, ya gyaɗa mata kai alamar ta bi shi. Kamar mara gaskiya haka ta bi bayansa, sai da suka ɗan yi nesa da gidan kaɗan, sannan ya waiwayo ya kalleta ya ce "Me ki ke nema a wurina?" Ta kalleshi ta sunkuyar da kai. "Ki yi mini magana, me ki ke nema a wurina? Meyasa ki ke sintirin zuwa in da nake? Idan so ki ke a kama ni, ki kawo su su kama ni mana, wace irin yarinya ce ke ne?" Yadda yake maganar cikin hargowa, sai da ta ja da baya, saboda tsoro. "Talk! Me ki ke so, waye ya turo ki?" "Ni ba wanda ya turo ni" ta yi maganar cike da tsoro. "Me ki ke nema?" A sangarce ta ce "Ni ka daina yi mini magana a haka, tsorata ni ka ke yi, ni ban san me zan ce maka ba"ta yi maganar tana kawar da kanta gefe. Ya tsareta da idanunsa, ita kuma taƙi ɗagowa, ta sunkuyar da kanta ƙasa tana haɗe fuska cikin tsoro. Ya sunkuyo dai-dai tsawon ta ya ce "Ki bani amsa" tayi shiru ta ƙi magana. Hakan ya ƙara hasala shi, ya buga ƙafarsa ya ce "Ki yi magana kan na saka ki yi ta ƙarfin tsiya" Cikin rauni ta ce "Na gaya maka, ni babu wanda ya turo ni, ni na turo kaina, kuma ni tsoro ka ke bani ban san ta ina zan fara ba, tsorata ni ka ke yi" Ba ta ƙarasa maganar cikin nutsuwa ba, ta ji hannunsa a wuyanta. "Naja'atu Bunkure, meye alaƙarki da ita? Ita ki ke yi wa aiki a kaina, da ita da Indabo ko?" Ba ta yi masa magana ba, sai idanuwanta da suka yo waje, ga hawaye na bin fuskarta, sai dai kallon da ta yi masa, ya sanya ƙirjinsa bugawa da ƙarfi, ya saketa ya ja da baya, yana dafe saitin zuciyarsa. Dai-dai lokacin Walid ya ƙaraso ya ce "Viper meyasa ka ke haka ne? Ban sanka da cin zarafin mata ba, meyasa ka ke ƙoƙarin farawa yanzu?" Ya nuna Nabila da yatsansa, amma ya kasa magana sai haki yake yi, saboda zuciyarsa ta ƙi nutsuwa. Ta ƙura masa ido, tana kuka. Kawai ya juya ya bar wurin, Walid ya ce "Sannu, kin ga abun da nake guje miki a kansa ko? Shiyasa na ce ki daina zuwa anyhow. Mun gode da gudunmawarki ga ɗan uwanmu, amma ki daina zuwan nan, ina tsoron yayi miki illa wataran". Ta girgiza kai ta share hawayenta ta ce "Ina da kafiya wasu lokutan, haryanzu ban ji cewar zan karaya ba, da ya bi ni a sannu, da zan yi masa bayanin abun da ya haɗa ni da Naja'atu Bunkure. Kawai ji nake ya zame mini wajibi na taimake shi, ina son sanin ƙarshen labarinsa, har cikin zuciyata nake son ba shi gudunmawa, na yi masa uzuri, wataran ba zai yi mini haka ba, bari na tafi. Ayyuka sun yi mini yawa ne sosai, amma ina nan zan je wurin likitan ƙwaƙwalwar, zan kuma dawowa" Walid ya girgiza mata kai ya ce "Rayuwarki fa, ke kanki zaki jefa kanki cikin hatsari" Nabila ta share hawayenta ta ce "Kar ka damu da ni, shi ɗin a ceto rayuwar sa da hankalinsa, a ƙwato masa hakkinsa, ba a san amfanin da zai yi wa al'umma nan gaba ba, ina son kamo bakin zaren lamarin ne, bari na tafi" ta juya ta tafi. Walid ya girgiza kai, duk haryanzu bai tabattar da manufar Nabila a kan Al'amin ba, amma a jikinsa yake jin ba zata cutar da shi ba. Ya koma gidan su, ya tarar da Al'amin ya cika yayi fam, ya kalle shi ya ce "Mai zamani ba ka kyautawa gaskiya, shi yaƙi ɗan zamba ne, ko da turotan aka yi, sai ka bari mu bi komai a hankali, haka Ƙanwata tayi ta fama da kai, da wannan zafin zuciyar ta ka, ƙarshe ta zame maka sanyin idaniyarka. Ka din ga bin komai a hankali, bamu san mai gobe za ta haifar ba, kar ka daki kwano. Ina son mu ƙara zurafafa bincike a kanta, wanda na yi bai gamsar da ni ba" "Mai laya" "Viper" "Ka ƙyale ni da maganar yarinyar nan" Walid ya ce "Ba zan ƙyaleka ba, sai ka fuskanci gaskiya Viper". Nabila tana tafe, tana mamakin dalilin da ya sanya Viper yake son kasheta wasu lokutan, amma meyasa ya rikice haka da ya ji ta ambaci Naja'atu Bunkure?. Gaba ɗaya al'amuran case ɗin Viper sarƙaƙiyarsu ta yi yawa, a labarin da Walid ya bata, ba ta ji in da Najar tayi masa wani abu ba, kodayeke haryanzu labarin bai kammala ba. Gida ta yi niyyar tafiya, dan kanta ciwo yake yi mata, amma kwana biyu ba ta haɗu da sumayya ba, kuma gashi ba ta bata labarin karonta da Naja'atu ba, dan haka ta kira nufi gidan radiyon su Sumayya. *** Ramma na zaune na karyawa take kallon Abdul, yadda ya sha kunu, yana video call da wani likita, yana yi masa bayani, a kan wani result na patient da ya turo masa, yanayin yadda yake bayanin ya tabattar mata da ya san abun da yake yi. Sai da ya gama sannan ya rufe tab ɗin, ya kalleta ya ce "Kalli gabanki kar ki lashe ni" Ta kwaɓe baki ta ce "Ban ga abun lasa a jikinka ba, jiki duk najasa". Cikin ko in kula ya ce "Haka dai ki ke zaune da ni" tayi guntun tsaki, ta cigaba da tauna a hankali. Can ta sake kallonsa ta ce "Abdul yasar" Ya ce "Your excellency" Ta ɓata fuska ta ce "Ba na son wata your excellency". "Ke ba abun alfaharinki bane ba, ace ke yarinyar deputy governor ce ba" "Malam ka daina zaƙewa ba zaka taɓa ci ba, ai shugaba nagari ake fata, kai idan ka zama shugaba ai ina ga sai ka halatta zina, tun da gaka bature, yahudawa ne abun koyinka" Ya girgiza kai ya ce "A'a iskancin nawa bai kai nan ba" Ramma ta ce "Ga wanda bai sanka ba ba, ni tambayarka zan yi, wai dan Allah da gaske kai likita ne? Mamaki nake yi" yayi mata banza yana shan tea. "Taɓ, kura da fatar akuya, ba su san har giya ka ke sha ba, ashe wataran zaka yi kisan kai, ko ma in ce kana yi. Saboda irinka wasu mazan suke raka mata asibiti, dan tsaf zaka yi wa matan mutane ɓarna tun da ka saba" yadda ya dire kofin yana kallonta ne ya sanya ta sha jinin jikinta. "Meyasa ba ki da ɗa'a?" "Saboda ɗa'a muhalli ne da ita, nan kuma ba wurin da ya dace na nuna ta bane" Ya jinjina kai ya ce "Haka ne, duk matar da na yi lalata da ita, ita ta kawo mini kanta, kar ki ƙara yi mini irin haka" "Nima ni na kawo maka kaina kenan ko? Baka da kunya ko kaɗan, sai dai idan ka gama kumburin ka fashe, har abada mutumin banza ka ke a idona, 'ya mace ba ta taɓa mantawa da wanda ya kawar mata da mutunci, ko da kuwa ta hanyar aure ne, balle ta mummunar hanya, irin wadda ka yi mini, wallahi ban da zuciyar musulunci da tuni na kashe kaina na huta, kaf danginmu babu mazinaci, amma ni kalle ni yanzu. Tsaki yayi, ya tashi ya zai fice. "Wallahi duk in da zaka je, Allah ya isata, na nan na bibiyarka har kabarinka" Dummm ƙirjinsa ya buga, ya waiwayo yana kallon ramma da ke ta uban kuka. Bai taɓa dana sanin aikata duk wani laifi da yake yi ba, sai a kan fyaɗen da ya yi wa ramma. Galibin saɓon da yake yi, tsakaninsa da Ubangiji ne, ba a taɓa tsayawa gaba da gaba, ana tsine masa da yi masa Allah ya isa ba, ya sha attempting ya mayar da ita, amma sai ya ji ba zai iya rabuwa da ita ba, kuma kamar yadda take yawan faɗa, ya riga ya gama lalata mata rayuwa, ba za ta yi daraja a idon jama'a ba. Motarsa ya shiga, ya tarar da wayoyinsa a ciki suka kwana, a buge ya dawo jiya tab ɗin sa ce kawai a cikin gidan, missed calls ɗin mahaifinsa babu adadi, ga na Naja'atu Bunkure, banda na mahaifiyarsa. Tunani yake yi ko lafiya ake yi masa wannan uban kiran hakan, shi ya san bai yi wani laifin ba balle ace. Haka ya ja mota, ya nufi gidan su, yana jin yadda Allah ya isan ramma, ke ƙara yi masa amsa kuwwa. Falon indabo ya nufa, ya na zuwa ya hau shi da faɗa, "Wane irin rashin mutunci ne zai sanya ka ƙi ɗaga waya tun jiya? Har na fara tunanin wani abun ne ya same ka? Kana can mashaya kana iskancin naka daka saba ko? Wallahi ka nutsu ba za ka lalata mini siyasa da shirina a banza a wofi ba, saboda shashancinka da rashin sanin ciwon kai ba, dole ka san abun da ka ke ciki ka shiga hankalinka" Zama yayi ya haɗe rai, yaƙi magana, har Indabo yayi masifarsa ya gama, sai da ya gama haki, sannan ya ce "Jiya Naja'atu ta zo mini hankali a tashe, yarinyar da ka yi wa fyaɗe, mutumin da aka ce shi yayi, wata lawyer za ta tsaya masa, ta je har office ɗin Naja'atu neman in da aka tsaya a case ɗin. Ina tsoron ranar da abokan adawa za su ɗagomu, ko su bankaɗo miyagun laifukan da ka ke aikatawa. Yanzu ina ka kai yarinyar yaya aka yi da ita?" "Ban sani ba, wace yarinyar nake magana a kai? Yarinyar da ka yi wa lalatar nake yi maka magana". "Amm...m...wai ita rahama?" "Kai ka sani, ina tambayar ka kana tambayata?" Abdul ya ce "Ba Naja ce ta je ba, zata ba su kuɗi a rufe zancen ba?" "Zan kife ka da mari wallahi, uban najar, ba ta je ba suka ƙi karɓar kuɗin, suka ce sai an karɓar musu hakkinsu ba? Ka ce mini zaka kashe yarinyar yaya ka yi da ita? Sannna yaya ka yi da uwar yarinyar, muddin case ɗin ya cigaba aka samu sani leakage mun kaɗe, zan iya asarar wannan wahalar ta wa, takarar ma ba zaka samu ba". Abdul ya dubi Indabo ya ce "Amma daddy ka riƙe muƙamai da dama a garin nan da ƙasar nan, kai yakamata ace ka zama governor nan ba ma deputy governor ba da ka ke ƙoƙarin ɗora ni a kai ba, ni da ka bar ni da sabgar siyasar nan takura mini za ayi na kasa sukuni yadda nake so". Indabo ya jinjina kai ya ce "Taɓɗijan, bilki anya ni na haifi yaron nan kuwa? Kina jin abun da yake faɗa?" Ta sha kunu ta ce "Wace irin magana ce wannan ka ke yi?" "Ki na jin abun da yake gaya mini, Abdul siyasa lissafi ce, idan ya ƙwace maka, babu wata fomular da zata yi maka solving duk wani hardship da zaka shiga. Na gama da jihar nan, sonake ka riƙa mini, sama nake tunani tawagarmu mu ƙarasa mamaye ƙasar nan, komai a lissafe nake yin sa". Abdul ya yi ajiyar zuciya ya ce "Yarinyar ta mutu ai, babarta ce take nan" "Ka tabattar?" Abdul ya jinjina kai. Indabo ya ce "Dole aje a nemo babarta, ita ma a kawar da ita, kar su ɓata mana aiki" Cikin tashin hankali ya ce "Ita ma wai kashetan za ayi?" Indabo ya ce "To me za ayi idan ba a kasheta ba? Sai asirinmu ya tonu kuma, sannan azo a fara neman mafita?. And na ɗaga komawata Abuja, sai Allah ya kaimu weekends, kai kuma zaka tafi jibi in Allah ya kaimu, akwai meeting da shugabannin jam'iyya na ƙasa da na jiha, sannan akwai meeting na musamman da deligates, dan dai a samu ayi nasara. Sai ka je ka yi shiri ka bar ni da sauran" Gaba ɗaya jikin Abdul ya yi sanyi, ya tsare mahaifinsa da ido. "Menene kuma ka tsaya kana kallona? Kafin ƙarshen watan nan kuma za a kai kuɗin aurenka, gidan party chairman kai da 'yar sa". Abdul ya murza goshinsa, saboda yadda kansa yake sara masa, gaba ɗaya ya rasa abun yi. *** A nutse sumayya take kallon Nabila ta ce "Arfa, idanunki sun nuna akwai damuwa, meyake damunki ne kamar ma fa kuka ki ka yi" kamar Sumayya ta soso mata wurin da yake yi mata ƙaiƙayi, kawai ta saka mata kuka. Sumayya ta ce "Matsalata da ke kenan, shagwaɓa arfa" ta share hawayenta tana zumɓura baki. Sumayya ta yi murmushi ta ce "Ƙila fa ba wani abin kirki ne ya saki kukan ba, ina jinki ko duk Najar ce, yaya ku ka yi da ita?" Nabila ta ce "Wannan ai azzalumar mace ce" nan ta gaya wa Sumayya yadda suka yi. Sumayya ta jinjina kai ta ce "To hakan ne ya saki kuka?" Nabila ta girgiza kai ta ce "Ke na gaji ne, kaina ya ɗauki caji, kin ga rashin mutuncin da barrister Kabir ma yayi mini duk saboda ita, ni kamar na karaya ma, amma wallahi ba zan janye ba" Sumayya ta yi dariya ta ce "Manya gatan wasa, karaya ba taki ba ce ba, akwai ƙalubale sosai a duk wata nasara da ake son cimma, dan haka ki yi haƙuri ki cigaba da addu'a, In sha Allah sai kin cika burinki a kan Naja'atu". "Wallahi sumy da kamar na karaya, amma ba zan karayan ba in sha Allah, sai na cika burina" "Yauwwa mutuniyar Viper" da sauri Nabila ta kalleta ta ce "Me ki ka ce?" "Mutuniyar Viper mana, ko shi yanzu kin ɗaga masa ƙafa, kin haƙura da nemansa kin koma kan fansarki ta naja'atu bunkure?" Nabila ta ƙurawa fuskar Sumayya ido ta ce "Al'amin mai dogon zamani" tayi maganar tana murmushi. Sumayya ta ce "Ban gane ba" "Kawai shaƙar da yayi mini nake tunawa ne, na kusa sheƙawa". "Amma haryanzu ba ki sanarwa DSP ba, yakamata ki tamakawa aikinsa fa" Nabila ta ce "Taɓ haka kurum ya gaya wa Abba, ya saka Abba ya harbe ni da bindiga har lahira, na je wurin ɗan daba, ba dani ba bari na tafi gida, marata ma ciwo take" Nabila ta tashi, sumayya ma ta tashi za ta rakata, a reception suka haɗu da P.A, gaban sumayya ya faɗi, ya din ga bin su da kallo, ita da Nabila. "Malam ka kalli gabanka mana, ji jaraba zai saka na faɗi" Nabila ta yi maganar cikin ɗaga murya tana kallon P.A Sumayya ta ce "Na shiga uku, haba Arfa, babba ki ke yi wa haka?" "To waye ya ce ya kalle ni?" P.A ya ce "Yi haƙuri, wallahi kallon sani nake yi miki ne, kina yi mini kama da wata da na sani" Nabila ta kwaɓe baki, yayin da jikin sumayya ya hau rawa. Ya ce "Sumayya wurinki na zo fa" gaba ɗaya sumayya ta rikice, dan kar P.A yayi wani abun da zai sanya Nabila gane wani abun, dan sharp brain ce da ita sosai. Nabila ta ce "Bar rakiyar kawai, ni na tafi sai mun yi waya, kuma ki daina ccacanza lambobi kina kirana, kamar wata mara gaskiya ko 'yar 419, idan na kira layinki ba zaki ɗaga ba, sai ki yi ta canza lamba" gaban sumayya ya faɗi, mussaman kallon da P.A yayi mata. Cikin yaƙe Sumayya ta ce "Layina ne yake bani matslaa, sai mun yi waya". P.A ya tasa ta a gaba, zuwa news room, in da take aiki, ya rufe ƙofa ya kalleta ya ce "Wato canza lamba ki ke yi ki yi waya da ita ko?". Sumayya ta ce "Ban san me zaku iya yi mata ba, dole sai na tantance abun zan din ga gaya muku a kanta". "Haka muka yi da ke? Kin zaɓi ki salwantar da rayuwarta kenan?" "Ba zan salwantar da rayuwarta ba, kuma babu abun da zai same ta sai wanda Allah ya ƙaddara mata, ku bani a hankali ai ina sanar muku da duk wani abu da take aikatawa kamar yadda ku ka buƙata. Menene na biyo ni nan kuma, ka yi mini magana a gabanta sai ta gane". P.A ya ce "Ta gane me? Muddin ki ka bari ta gane, sai ta zama gawa, an sanar mini ta zo ne, kuma na san muddin ta zo, wani muhimmin abun ne ya kawo ta. Me yake faruwa? Dan kar ki yi zaton ke kaɗai ki ke yi mana aiki, duk motsinki kema ana saka mana ido a kai". Sumayya ta yi ajiyar zuciya ta ce "Zauna mu yi magana". Nabila kuwa bayan ta fito harabar radiyon, still motar nan ta sake gani, wadda aka taɓa bin ta da ita, ta ganta a law firm ɗin su, yanzu ma gata a gidan rediyon su Sumayya, kuma lambar motar ce ta sake tabattar mata da motar ce dai. Wani guntun murmushi ta yi ta ce "Bari dai na ga ƙwal uwar daka". *** Ramma ba ta sake ganin Abdul ba sai can dare,  ba ta yi zaton zai kulata ba ma, ta ɗauka fushin da yayi ne ya hana shi dawowa, dan har ta fara bacci, ta ji motsinsa a bedroom ɗin. Ta buɗe ido ta kalleshi, ta ga bai kulata ba. "Kayi dare da yawa yau" ya waiwaya ya kalleta ya ce "Idonki biyu?" "A'a motsinka ne ya tashe ni" "Barin gidan nan zamu yi, gobe in Allah ya kaimu" cikin rashin fahimta ta ce "Saboda me?" "Wani dalili kawai, zan yi tafiya ne na sati ɗaya" "Kuma ka tafi ka bar ni nikaɗai?" Ya ce "Eh babu abun da zai same ki, can zamu koma gaba ɗaya, bana son a gano ki a nan". Ta taɓe baki ta ce "Kana nufin dai haka zan cigaba da zama kenan?" "A'a ina tunani a kan zaman mu" Tayi shiru, ta gyara kwanciyar ta, ta cigaba da baccinta. Juya tayi, ta ganshi a zaune, yana hana haɗa ƙwayoyi, ya ɓalle wannan ya ɓalli waccan. Matsawa ta yi ta ƙwace ta ce "Ba zaka sha wannan ƙwayoyin ka mayar da ni jakarka ba, ba zai yiwu ba, wallahi ko na bar maka ɗakin" a sanyaye ya ce "Ba wanda ki ke tunani bane ba, damuwace ta ɗan yi mini yawa, bacci nake son na yi" ta saka hannu ta kwashe packets ɗin ta ce "Kai kamar ba likita ba, anya ma ba likitan bogi bane ba, haryanzu ina tantama babu likitan kirki da zai yi abun da ka ke yi". "Ke ba zaki gane ba ne, ki bani kawai idan ba haka ba, baccin ba zai yiwu ba". "Aikuwa sai dai kar ka yi" ta watsa su bayan gadon, ta gyara kwanciyar ta. *** Nabila tana zaune, tana kaɗa ƙafa tana cin gugguru, ta na zancen zuci, ta kalli wayarta da take silent, sai haske take yi, ta saka hannu ta ɗauka, ta saka a kunnenta. "Hello barka da dare" A hankali ta ce "Yauwwa" "Ya gida aiki?" "Alhamdilillah" "Na ce ina da ƙorafi, a taimaka mini an ce na je office, na je sau biyu ba kya nan" Ta yamutsa fuska ta ce "Wake magana ne?" Ya ce "Ni ne" "To kai wa?" "Bawan Allah, ni ne na kira ki rannan. Wataƙila ina da magana mai muhimmanci da ke". Nabila ta yi guntun tsaki ta ce "Da maganar mai muhimmanci har haka, da ba a waya zaka tsaya kana zagaye-zagaye ba". Ta katsewayar, tana cigaba da ɓata fuska. Lambar Viper ta kira, ta na jiran ya ɗaga, har ta sare da zai ɗaga, ta ji ya ɗaga wayar. Tayi gyaran murya ta ce "Ka na ji na? Na san ma kana ji, ba magana zaka yi ba. An ce baka taɓa mata, amma ni kullum burinka ka kashe ni, ka yi ta shaƙe ni, ko cikakkiyar lafiya ba ni da ita, idan ka yi haƙuri ka ba a hankali zan yi maka bayanin komai, amma ka fiye zafin zuciya haryanzu maƙogwarona kamar an shaƙeni da ƙarfe nake ji" ta yi maganar har da kukan kissa. Yayi shiru yana sauraren ta. "Ba zan yi zuciya na daina zuwa ba, har sai ka gaya mini sauran labarin nan, na ji ina 'yar madara take, ina son saninta, akwai abubuwan koyi da yawa a rayuwar ta. Zan sake dawowa in sha Allah, amma ka rage zafin rai dan Allah, mu yi magana ta fahimta" Nasir ne ya shigo ɗakin unexpected, ta ɗaga kai ta kalleshi, ya ƙura mata ido. Ba ta canza daga yadda take ba, ta ce "Sai anjima, zamu yi magana" ta katse kiran ta kalli Nasir ta ce "Yaya shigowa ba excuse?" "Da wa ki ke waya?" Ta gyaɗa kai ta ce "Wani ne" "Wani wa?" "Is confidential" Ya ƙura mata ido ya ce "Confidential as how?" "Haba Yaya, client ɗina ne fa" "Amma ki ke wannan kashe muryar?" Ta ce "Ikon Allah, to ai he's not just a client, ammm" ba ta ƙarasa ba ya juya ya fice, ta yi ajiyar ta ce "Ohh ni Nabila, yaya ai sai dai ka yi haƙuri" Walid ne ya shigo ɗakin, dawowarsa kenan, ya tarar da Viper, a ɗakinsa, yana goge wuƙarsa sweazland. Ɗan mama kuma na zaune a gefensa. Zaro ido ya yi ya ce "Me zan gani haka? Viper waye ya ɗaukko wannan wuƙar, ya kawo maka?" Al'amin yayi shiru yana jujjuyata a hannunsa. Ya kalli ɗan mama da yake sunkuyar da kai, aikuwa a fusace ya saka ƙafa ya daki ɗan mama ya ce "Amma an yi shegen yaro, wallahi baka da mutunci ɗan mama, uban wa ye ya ce ka ɗaukko masa wuƙar nan?" Ɗan mama ya ce "To wai ya zan yi dan Allah? Cewa yayi sai na ɗaukko masa, kuma Oga liti ne ya ɗaukko ya bani, wai operation za su fita gobe, Madaki yana cikin gari" Walid ya din ga ɗurawa Ɗan mama ashariya, ya juya ya nufi Viper, Amma Viper ya miƙe tsaye, ya fito da harshen sa waje ya mayar. Walid ya nuna kansa ya ce "Ni zaka sakawa ƙarfe?" "Ƙwarai, muddin ka yi ƙoƙarin dakatar da ni, wallahi jininka za ta sha, ai na gaya maka ka nesanta yarinyar da ni, muddin ina ganinta ba ni da wata nutsuwa, dan haka ba ka da ikon, dakatar da ni". Walid cikin ɓacin rai ya ce "Hanyar da muke ƙoƙarin bi, ba mai ɓullewa ba ce, ka yi haƙuri" "Shhhh" ya yi maganar tsare Walid da ido. "Dalla matsa, ni zaka yi wa barazana, ka je ka yi duk abun da ka ga dama, na daina shiga harka, tafiya zan yi ku ƙarata da kai da su litin, mu gani idan hanyar za ta fishshe ku" Suna cikin faɗa liti ya shigo, suka ya tarar da su, liti ya ce "Kai walid, ba zaka hanamu abun da muke so ba, ka hanamu motsawa, wancan banzan madakin, yana ta rashin mutunci a gari, wallahi sai mun ɗauki fansa" Walid ya fice ya bar musu gidan cikin matsanancin ɓacin rai. *** Abdul ne da ramma suke tafe a mota, tana ta kallon hanya, ya yi locking ɗin motar, ga glass ɗin ta tint ne. "Wai tafiyar nan ba zata ƙare ba, ni fa na gaji". "Eh, cinikinki zan je na yi na sayar" ta harare shi, ta cigaba da kallon titi. Wata unguwa suka yi, babu gidaje da yawa a wurin, sai tsilla-tsilla, kuma manya manyan gidaje ne, na alfarma a rukunin. A ƙofar wani ƙaton gida ya tsaya, aka buɗe masa gate, ya shiga, wasu irin manyan karnuka na ta kai komo a harabar gidan, ya zagaya yayi parking, ya cire lock ɗin motar, ta buɗe ta fita. Shi ma ya fito, ya buɗe boot, ya ciro akwatuna, ya ce "Mu je" "Yanzu da ka mayar da ni gida, gara ka sake kawo ni nan?" Yayi gaba ya ce "Idan karnuka suka cinyeki, kya taho" ta bi bayansa tana rarraba ido, gida mai kyau na alfarma. Saman bene suka hau, ya kaita wani katafaren bedroom, ya ce  "A nan zaki zauna, zuwa lokacin da zan dawo, kafin nan na samo mafita, zaki iya shiga ko ina, an ajiye duk abun da ki ke buƙata, sai dai ko haraba ba zaki fita ba. Zan ajiye miki waya duk abun da ake ciki, ki kirani ko idan kina buƙatar wani abu, wayar lambata kawai zaki iya kira". "Wai dan Allah nikaɗai zaka bari a gidan nan, ni tsoro nake ji wallahi" "Ki yi haƙuri mana, ba zan daɗe ba, na ɗan lokaci ne, zaki yi missing ɗi na ko?" Yayi maganar yana kissing ɗin goshinta. Kuka take yi sosai, ya rungumeta yana rarrashin ta. *** Yau ma kaca-kaca Walid ya yi da su Viper, Liti yana supporting ɗin Viper a kan iya wuya, kawai su afka su ɗauki fansa. Duk yadda walid ya so fahimtar da su, suka ƙi fahimta. Nabila ta fara gane kan hanyar zuwa gidan su Viper, kanta baya kullewa kamar da. Babu tsammani ta yi karo da Walid, ta ja ta tsaya, ta zata zai yi mata masifa, ta ce "Ina wuni?" "Lafiya ƙalau" "Amm yana ina?" Ya nuna mata dutsen da yake can gaba, ya ce "Yana can, amma ki daina wahalar da kanki, taurin Al'amin yayi yawa, an ɗaukko masa wuƙarsa, zai je ya yi gaba da gaba da madaki yau, ki ƙyale shi kawai" Ta girgiza kai ta ce "A'a, zan jarraba sa'ata" tayi gaba ta nufi in da dutsen yake, ba ta ƙarasa ba ta hango shi, a zaune a gefen bishiya, cikin inuwa yana ɗan kaɗa ƙafa, ya na shan sigari. Ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi ta ce "Barka da rana" bai amsa ba, ta saka hannunta, ta zare sauran karan tabar hannunsa ta ce "Ayi mini uzuri, ba na son hayaƙi, mara zuciya na sake dawowa. Dan Allah kar ka shaƙe ni, magana zamu yi ta fahimtar juna" Ya ɗaga kai ya kalleta, ya yinƙura ya miƙe, ita ma ta tashi ta tsaya a gaban sa, ka saurare ni ko sau ɗaya ne, zafin zuciya da gaggawa shi ya sanya ka rasa da yawan mutane masu muhimmanci a rayuwarka". Sweazland ya saka mata a wuyanta, ya ce "Gargaɗi na ƙarshe, ki rabu da ni, ki fita daga rayuwata". Ta kalli yadda wuƙar ke ƙyalli a saitin wuyanta ta ce "Sai na ji ƙarshen labarinka, na ji wa ka kashe? Kuma ina jauhar da abun da yake cikinta?" Ya kalleta ita ma cikin ƙwarin gwiwa ta cigaba da kallonsa, duk da ƙasan zuciyarta a tsorace take. "Ki daina kallona a haka, meyasa ki ke son ki zama raunina ne?" yayi maganar muryarsa na rawa. Ayshercool 08081012143 53 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 "Meyasa zan zama rauninka ne? Wallahi ba cutar da kai zan yi ba, ba na nufin yin hakan. Idan niyyata kenan a baya yanzu na canza tunani, dan Allah ka fahimce ni". Ya sauke numfashi ya ce "Me ki ke buƙata?" Ta ce "To dan girman Allah mu zauna, sai mu yi magana, ba dan ni ba" Ya koma ya nemi wuri ya zauna, ta yi ajiyar zuciya, tare da ƙara jinjinawa Jauhar. Ita ma ta zauna, ya ce "Ina jinki" "Kamar yadda na gaya maka da farko, na yi nadamar abun da nayi, wallahi ba ni da niyyar cutar da kai ko kaɗan. Dan Allah ka yi haƙuri, a shirye nake na taimaka maka, na ƙwato maka hakkinka, da na matarka kai har ma da na yaronka Nura, ko hakan zai sanya na baya su kuɓuta daga irin abun da ya faru da ku, amma hakan ba zai yiwu ba, sai ka ƙarasa mini labarin abun da ya faru" "Bana buƙatar taimakonki, zan yi abun da nake ganin ya dace" Ta girgiza kai ta ce "Bari, ɗan hakin da ka raina, shi ka iya tsole maka ido, ni ko ba dan kowa ba, dan 'yar uwa jauhar, wallahi labarinta kawai da na ji ta tsaye mini a rai, ina sonta saboda girman Allah, rayuwarta abun tausayi ce kuma abar koyi, har cikin zuciyata nake jin raɗaɗin abun da ya faru, ban rayu da ita ba, amma halayenta sun yi mini, sun burgeni kuma duk in da na zauna, zan buga misali da su. Dan Allah ka yarda da ni, ka bani haɗin kai" Kallon hawayen da take yi yayi, ya ji ina ma shi ne ya samu wannan damar, yake zubar da hawaye ya ji sanyi a ransa. Duk da yadda take ƙular da shi, amma hawayenta ya sanya zuciyarsa motsawa, da jin kamar ya amince mata, ko da cutar da shi za ta yi, tun da ta nuna tausayi da ƙauna ga matarsa, haƙiƙa ta samu wani mutunci a idonsa. Ta share hawayenta ta ce "Na bibiyi file ɗinka na shari'a, an rubuta kisan kai ake tuhumar ka da shi, wa ka kashe? Garin yaya ka yi kisan kai? An kama ka an sake ka, kuma an dawo ana nemanka". Ya kaɗa kai ya ce "An bar jaki ana dukan taiki ba, sun fuskanci ƙarfen cikin wuta ne ni, na fi ƙarfin hannu. Shekara ɗaya, biyu, uku, huɗu, biyar, Naja'atu Bunkure" yayi maganar yana kallon yatsunsa. Cikin zaƙuwa ta ce "Me ta yi maka? nima da ka ji ina waya, na yi zancenta, wata yarinya aka yi wa fyaɗe ta shiga case ɗin ta karɓa, kuma an yi wa wani dattijo sharri wai shi yayi mata, alhalin ainihin case ɗin wani ɗan babba ne yayi, wallahi abun da ya sanya na ambaceta kenan a maganata, ba wai aiki nake yi musu ba. Ka yi mini magana dan Allah. Bana fatan ka ɗauki fansa ta hanyar da ba ta dace ba, ba zaka taɓa hucewa ba, ka bari rayuwarsu ta tagyayara tukuna. One of the biggest fear na masu mulki, shi ne rasa ƙwarin gwiwar su daga mutane, yayin da asirinsu ya bankaɗu mutane suka daina yarda da su. Indabo yayi ƙarfin da ka tunkare shi kai tsaye, ba zai yiwu ba. Kisan mummuƙe yakamata ka yi masa, dan Allah ka gaya mini me Bunkure tayi maka, hakan zai taimaka mini a wurin Shari'a". Viper ya ce "Ba na buƙatar wata shari'a, ko wani ya ƙwato mini hakkina, shari'a ita ta fara cin zarafina, babu komai a harkar nan ta ku, sai zalunci da son zuciya, taimakon wanda ku ke so, da tozarta wanda ya gaza baku kuɗi duk gaskiyar sa". Taji daɗin yadda yake yi mata magana, dan bata taɓa zaton yana magana haka ba. "A'a kar ka ce haka dan Allah, Dan Allah da gaske kisan kai kayi?" Ya ce kalleta ido cikin ido ya ce "Eh, kisan kai nayi, Naja'atu Bunkure made me confess it" Ta haɗiye wani abu, ta girgiza kai ta ce "Ba zan taɓa yadda da hakan ba, labarin Viper da na ji, bai taɓa kisan kai ba, wa ka kashe?" Tashi yayi, ya ɗauki wuƙarsa yayi gaba, kamar mayya ta tashi ta bishi cikin sauri, amma saurinsa ya ninka nata, dan haka ya rigata isa cikin gidan, kafin ta ƙarasa har ya shiga ɗaki ya rufe kansa. Ta taga ta tsaya tana leƙawa "Dan Allah ka daina bani bayani guntu-guntu ka ƙarasa mini, hakan zai taimaka mini wurin sanin ina zan kama, wa ka kashe dan Allah?" Ya tsaya ƙyam ya juya mata baya, ya dafa jikin bango, zuciyarsa tamkar ruwa na tafasa a ƙasan gagarumar wuta, haka wani Irin zafi ya din ga taso masa daga ƙirjinsa zuwa ƙwaƙwalwarsa. Nabila ta din ga bubbuga ƙofar, tana yi masa magiya ya buɗe, amma yaƙi, ta koma ta window, ta ga tuni ya fara ɗurawa kansa allura. "Dan girman Allah ka bari, lafiyarka da ta ƙwaƙwalwarka, wannan ba mafita ba ce ba, dan Allah kar ka illata kanka". Liti ya ce "Zo ki fita, koma uban menene ba ke ce sila ba, uban waye ya ce ki zo, yau ya tashi da 'yar walwala kawai kin zo kin kuma tunzura shi". Cike da tsananin damuwa, da tashin hankali ta baro gidan, tana tunanin to ita menene laifinta, da suke cewa ita ce sila idan ya ganta yake burkicewa. *** Ramma ta zubawa Abdul ido, ya haɗa akwatin sa tsaf, ya kalleta ya ce "Ƙarfe huɗu jirgina zai tashi, dole na shirya da wuri, akwai in da nake son zuwa kafin na tafi" Ta turɓune fuska, tayi masa shiru. Ya zauna kusa da ita, ya ɗago haɓarta yana kallon fuskarta ya ce "Ya dai?" "Ni dai kar ka tafi dan Allah, tsoro nake ji wallahi, nikaɗai zan zauna a nan dan Allah" Ya kwantar da murya ya ce "You start missing me?" Ta girgiza masa kai alamar a'a. "Your excellency, ba iya tsoro ne a idonki ba, missing ɗina zaki yi" Ta ture hannunsa ta ce "Allah ya kiyaye, ni gaskiya tsoro nake ji" Abdul ya ce "Tafiyar nan dole ce, sannan ina son na je garinku yau, zan ce wa mamanki kina gaisheta" Ta marairaice ta ce "Dan Allah ka mayar da ni mana" Ya girgiza kai ya ce "Ba yanzu ba" "Nan gaba zaka mayar da ni?" "Eh to, sai ƙura ta lafa" tayi shiru tana wasa da yatsunta. "Ki yi haƙuri, zan dinga kiranki kullum muna magana, idan da wani abun ma sai ki gaya mini, na ajiye miki komai na amfani a kitchen, ai kin iya girki ko?" Ta jinjina masa kai alamar eh. Ya ce "Yauwwa your excellency" ya tashi ya shiga wanka, yana ta shiri, ya zauna a gefen gado yana shafa mai, ta riƙe shirt ɗin sa tana kuka. Nan ya lalace a wurin rarrashin ramma, "Wai wannan kukan duk dan kar na tafi ne?" "Ni ina ruwana da tafiyarka, tsoro nake ji ne" "Ƙarya ki ke yi rahama, faɗi gaskiya dai" "Ni ba na ƙarya" tayi maganar tana murguɗa masa baki sannan ta ce "Kuma wallahi ka bi mata Allah ya isa" bai san lokacin da ya ƙyaƙyace da dariya ba, har sai da ya bata haushi. Har ƙofar falon ta rako shi, tana kallonsa, ya kasa gane kallon me take yi masa har haka, yayi mata sallama, ya sanya mukulli ya kulleta, ya ja akwatinsa. *** Kan Nabila tamkar zai yi bindiga, ta rasa abun da yake yi mata daɗi, haka ta koma jiki babu daɗi, kanta fal tunani daban daban. Har ta shirya, zata ci abinci, kawai ta tuna kwana biyu ba ta haɗu da Nasir ba, kuma ba ya shiga sabgarta, gashi tana son sanin a ina ya tsaya a binciken Viper, saboda duk yadda za ayi ba ta son ya gano Viper ba ta gama na ta binciken ba, idan ya so ko kotu za a shiga, ta shiga da ƙwarin gwiwar ta. Gaba ɗaya mayar da hankali a kan aikinta ya sanya, ba ta shiga sabgar yan gidan, hakan ya rage yawan faɗace-faɗace da suke yi da 'yan gidan. Ta fito falo, dan ta gaji da zaman ɗaki, abubuwa duk sun dameta, sai ga Nasir yayi sallama a falo, ta amsa sallamar tana kallon sa, amma ya basar da ita ya nemi wuri ya zauna. Ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi ta ce "Sannu da zuwa" "Yauwwa" ya amsa mata a ciki. "Wai me na yi maka ne ka ke wani share ni?" Tayi maganar a shagwaɓe. Rasa me zai ce mata yayi, yai shiru, ya kawar da kansa gefe. Ta zagaya in da ya kawar da kan ta ce "Me na yi ne?" "Bakomai". "To ka kula ni mana". Nasir ya ce "Na gaji, kar ki dame ni dan Allah" "Sai na gaya wa Abba kana hantarata" Ya ce "Sai kin dawo" ta rausayar da kai ta ce "To ni dai ka yi haƙuri, dan Allah" ya kalleta ya ce "Ya wuce" "Yauwwa DSP, to ya ake ciki ya aikin?" Ya gyara zamansa ya ce "Alhamdilillah, mu na ta fama ya naki?" Ta kwaɓe baki ta ce "Babu daɗi, duk na gaji, da fa ajiye aikin zan yi, aka bani haƙuri" Nan ta bashi labarin abun da barrister Kabir yayi mata. Nasir ya ce "Ke baki da haƙuri ne, shiyasa wasu lokutan ba kya cin ribar abubuwa, ki daina gaggawa" "Ai abun ne ya bani mamaki, daga zuwana wurinta, har an kira barrister Kabir an gaya masa, baka ga abun da ya yi mini ba, da cewa na yi sai na gaya wa Abba ma". Nasir ya ce "No, ba za ayi haka ba, duk abun alkhairin da yake yi miki, sai a kan laifi ɗaya ki yi fushi" "To meyasa zai yi mini tijara a kan wata Naja". Ya ce "Hakan yana alamta miki cewa, kin ɗaukko gagarumin abin da sai kin yi kyakywan shiri na gaske". Tayi ajiyar zuciya ta ce "Haka ne, ya ake ciki da naka aikin, yaya batun case ɗin Viper, akwai cigaba kuwa?" "Wallahi ba wani cigaban kirki, ina da ta fafutuka, gashi sai hura mini wuta ake yi" "Kai abun babu daɗi, but you can do it, na yarda da kai ai". Mama ce ta fito fuska a haɗe ta ce "Nasir menene haka?" Ya ce "Mama a ina?" "Ban sani ba, uban me ka ke zaune a nan ka ke yi? Ka dawo gida tun ɗazu, amma ka gagara shiga inda nake?" Nasir ya ce "Wallahi nayi tunanin bacci ki ke yi, shiyasa na yada zango a nan muke magana da Arfa, yi haƙuri" Nabila ko a jikinta, ta sake gyara zamanta ta kwanta sosai a kan kujerar tana danna waya. Mama tayi mata wani mugun kallo, ko a jikinta, sai ma wani irin murmushi da tayi. Messages aka din ga turowa Viper, da private numbrn nan, da ake kiransa da ita. "Muddin ka cigaba da biyewa yarinyar nan, asirinka zai tonu, kuma zata iya rasa rayuwarta a dalilinka, ba ka da sa'a wasu lokutan, kar ka bari ta zama raunin da maƙiyanka za su yi amfani da ita, wurin cimmaka har maɓoyarka" Ya din ga jujjuya wayar, yana sake tunanin waye wannan, kowaye ya sanshi, ya kuma san in da yake, kuma yana ankare da duk abun da yake yi, amma meyasa yaƙi bayyana kansa?. Kiran Nabila ne ya shigo wayarsa, tana zaune hannunta riƙe da waya a kunnenta tana kiran lambarsa, babu tsammani ta ji ya ɗaga. Ta kalli agogon ɗakinta, ƙarfe goma daidai na dare. "Barka da dare, duk da ba amsawa zaka yi wa ba. Amma ina fatan kana lafiya? Na kasa jurewa ba zan ɓoye maka ba, ban ji daɗin yadda na baro ka ba, muna cikin magana ka tashi ka tafi, kuma ka je ka na yi wa kanka allura, gaba ɗaya ban ji daɗi ba, dan girman Allah ka rufa mini asiri kar ka yi wa kanka illa, ka bari mu yi nasara mu kamo bakin zaren. Na san maybe ka raina gogewa ta, kuma kamar ba zan iya ƙwato maka hakkinka ba, amma na san Allah yana tare da mu, dan Allah ka daina shan abun da zai yi maka illa, ba na jin daɗi, na san yayata ma 'yar madara ba zata ji daɗin hakan ba, dan gaskiya sai ta matsa mini na shigo, daga ni sai a rufe. Saboda son da nake yi mata make son mu kasance tare, idan na shiga gidanta, kaga gani ga ta, in ƙara koyon halayenta, in ƙara sonta, amma gaskiya ayi mana adalci, saboda kishi ne da ni sosai da sosai fa, kuma alamu sun nuna mini kana sonta da yawa" Kamar mai sauraren karatu, haka ya nutsu yana jin ta, ɗan mama da yake kusa da shi, har kuma leƙa idonsa yake yi, ya ga reaction ɗin da zai yi, tare da jinjina rawar kan Nabila, a gaban Viper ko ƙwaƙwaran motsi ba ta iya yi, amma ta sameshi a waya, sai karairaya take yi tana shagwaɓa. Ta sauke numfashi ta ce "Bari na ƙyaleka, amma yakamata na san ƙarshen labarin nan, saboda na san yanayin shirin da zan yi, kuma kar sai na gama zaƙewa 'yar madara duk kirkinta ta ce ba zan shigo mata gida ba, dan ni gaskiya idan ba gidanta ba sai rijiya. Sai da safe take care" tayi maganar tana ajiye wayar, cikinta na kaɗawa saboda ita kanta ta san ba ƙaramar kasada take yi ba, abun da take yi. Amma hanyar da matarsa ta bi ta iya samun kansa da farko, dole ita ma ta bi, domin cimma nasara, saboda gaba ɗayansa hukuma ne, sai da rarrashi. *** Sanye yake da face mask, yana tuƙi a hankali, saboda yadda hanyar ta ƙara lalacewa, a ƙofar gidan su ramma yayi parking, ya fito ya tsaya a waje yayi sallama, amma shiru, ya shiga cikin gidan sai dai tsakar gidan babu kowa, ƙofofin ɗakin duk a buɗe. Ya ɗan jira ko za a shigo, ko fita tayi, amma shiru, ba ta dawo ba. Ya fita ya tambayi maƙwabta, suka sanar masa kwanaki huɗu kenan, su ma ba su san in da ta tafi ba, ba ta yi wa kowa sallama ba. Yanayin gidan ya tabattar masa da ba fitar nutsuwa tayi ba, ya lissafa shi yanzu kwanaki uku kenan, da mahaifinsa ya kira shi yai masa magana a kan batun ramma balle ya ce ko mahaifinsa ne. Yayi shiru yana tunanin to garin yaya haka, ya za ayi ta fita ta bar gida a buɗe haka babu kowa, tsawon kwanaki huɗu, ba ta yi wa kowa sallama ba, lallai akwai wani abu a ƙasa, yanzu me zai cewa ramma? Ya tambayi kansa. Lallai akwai wani abu a ƙasa, gashi lokaci na nema ya ƙure masa, ƙarfe huɗu zai tafi. Saif ya kira a waya, ya sanar masa halin da ake ciki, saif ya ce "Kuma baka tunanin ko guduwa tayi, ko kuma daddy ne yayi mata wani abun?" Abdul ya ce "Bana tunanin haka, shekaranjiya yayi mini zancenta, da shi ya saka aka ɗauke ta zai gaya mini, na rasa wani lissafin ma yakamata na yi" Saifu ya ce "Ka tafi kawai, zan tsaya na sake bincikawa, in Allah ya yadda ba wani abu". Ya ce "To shikenan, ina saurarenka dan Allah" ya ajiye wayar yana cigaba da tunanin lamarin. *** Abdul yana sauka a Abuja, sai da ya kira Ramma, ya ce mata ya sauka, sai dai ba ta amsa masa ba sai cewa tayi "Yaya ka baro mini mama? Tana nan lafiya? Ta tambaye ka yaya nake?" "Ni ba zaki tambayi ya na sauka ba, sai mama kawai?" "Dan Allah ka gaya mini, ko na ji daɗi" Abdul ya ce "Zan gaya miki da daddare idan na huta" ya katse wayar yana fargabar ranar da ramma ta san halin da ake ciki, bai san ya zai yi ba. Ya san duk laifin shi zata ɗorawa. *** Katafaren falo ne, ya sha ado da kayan alatu na zamani, manyan mutane ne su uku, zaune a falon wanda kaf ɗin su sanannun fuskoki ne da su a ƙasa. Kayan shaye-shaye ne a gaban su, suna sha suna hira, gefe ga kayan marmari. "Distinguish ma'aruf Indabo, ya ake ciki ne gaba ɗaya baka walwala?" "Komai ma ya dame ni ne, Abdul sai so yake yi sai ya watsa mini lissafi, da ƙyar na yaƙo shi, ya tafi Abuja, zaman taron nan, nima gobe in Allah ya kaimu zan tafi birnin tarayyar" "Ya salam, wai meyasa Abdul yake haka ne? Ya san wahalar da muka yi kuwa kafin mu zo nan, shi me yake damunsa ne?" Indabo ya kora ruwan lemon da yake cikin kofin hannunsa, ya ce "Oho masa, gaba ɗaya na kasa gane kansa, ina tsoron Allah ina tsoron ya aikata wani abun da zai yi dalilin takarar nan, amma ina nan na kafa na tsre ina monitoring activities ɗin sa". "Ohh Allah ya kyauta, ya batun wannan yaron ne da ake nema?" Indabo ya girgiza kai ya ce "Hmm honorable kenan, wallahi kullum da shi nake kwana nake tashi, kamar wani iblishi, ya gagara kamuwa, na rasa uban da yake tsaya masa, sai dai na samo wata yarinya da nake son ayi masa tarko da ita, to ita kanta yarinyar ba ta da cikakken saiti, wata barrister ce, 'yar wani tsohon soja, idan na matsa zata iya tona mana asiri, na saka ana yi mini monitoring ɗin ta, ta hanyar ƙawarta. Saboda wani furuci da tayi. Duk dai na ga hanyoyin ba sa yi mini sauri, na san dole yaron nan bakam yayi mini, at any cost sai na canza dabara, wadda za ta ɓulle mini da wuri, na kashe Aminu na huta" Haka suka cigaba da jimantawa, tare da tattaunawa da neman mafita, suna yi suna shaye-shaye. Ramma tana duƙunƙune a cikin bargo, karnukan estate ɗin, da na gidan sai haushi suke yi. Video call suke yi da Abdul, ta ce "Ba ka ce mini komai a kan mama ba" "Mama tana lafiya, ta ce a gaishe ki" Ta ce "Hmm, to ya take, tana cikin damuwa ko? Tayi kuka?" Ya ce "A'a, na bata tabbacin kina nan lafiya, har hotonki na nuna mata" Ramma ta ce "A'a hankalinta ba zai taɓa kwanciya ba, ka manta rashin ɗa'ar da ka yi mata, ranar da ka je ka tabattar mata da kai ka keta mini haddi, kuma ka tafi da ni, ai a yanzu idan akwai wanda ta tsana bai wuce ka ba, kodayeke akwai wanda suka yi mata wasu laifuffukan" Yayi shiru jiki a sanyaye ya ce "Laifin da suka yi mata irin nawa ne? Ai na nemi afuwarta" "Ta ina ka nemi afuwarta? Hmm ta ce ta yafe maka ne? Kai baka ganin girman laifin da ka aikata fa saboda mu talakawa ne kana da kuɗi. Mama ta sha wahala sosai, gashi duk mun ɗaiɗaice, kaga ƙanina sani daka je?" Ya girgiza mata kai ya ce "Ina ga yana makaranta" "Shikenan, sai da safe, bari na rintse idona ko zan yi bacci, haushin karnukan nan ya isheni" Ya ce "Ni kuma sanyi ne nan ya dame ni, da muna tare da kin bani ɗumin jikinki" Cikin tsiwa ta ce "Saboda gani heater ko?" Ya ce "No, jikinki akwai ɗumi sosai, da duk ba zan ji wannan sanyin ba" "Sai da safe" "Dan Allah ki tsaya ban gama ganinki ba" ta ce "Sai kuma ka yi ai" "Miƙo bakinki na yi miki kiss" "Ba na so" tayi maganar bacci yana kwasarta, tana lumshe ido. Ya ce "Rahama" "Na'am" ta amsa tana buɗe ido da kyar. Sai kuma yayi shiru yana cigaba da kallon fuskarta, har bacci ya kwasheta, yana kallonta, tausayinta ya din ga ratsa zuciyarsa. *** Yau weekends, Nabila tana gida, tana kai komonta, ta bayar da wankinta ayi mata, ta fito harabar gidan tana zagawa, Nasir ya fito da shirin fita. "DSP sai ina? Ko zance za a tafi rana tsaka" "Wurinki zan zo zancen" tayi dariya ta ƙarasa gabansa ta ce "Ina zuwa yanzu?, La'asar ta kusa?" Ya kalli agogon hannunsa ya ce "A kan Viper ne" Cikinta yayi ƙuuu, amma ta maze ta ce "Ya ake ciki?" Ya ce "Eh to, na canza dabara ne, a yanayin neman nasa, mun riga duk mun yi connecting da mutanen unguwar su, an ce yana zuwa gidansa da ya zauna, to kwana biyu bai je ba. Abokin faɗansa da na kama kwanaki madaki, an ce ya dawo yana cikin gari, akwai ƙishin-ƙishin na zai iya zuwa unguwar, neman rigima da shi madakin, duk mun baza komar mu, akwai wurin shayin yaransa, an ce ma wurin nasa ne, zuwana biyu wurin cikin fararen kaya, an kwatanta mini wani yaronsa Walid, na haɗu da shi a wurin, amma ko kaɗan ba sa zancensa a wurin. Da na so na zunguro zancen daba ma, na kama sunansa, cewa suka yi na tashi na fita. Ina kyautata zaton wannan Walid ɗin ya san in da yake, motsinsa zan sakawa ido sosai, ana ta yi mini binciken ina yake da zama, da a unguwar suke zaune, amma tun da Viper ya bar prison, sun daina kwana a unguwar sai idan za su yi aikin rabawa ƙanan dealolinsu wiwi. Ba zan motsa da wuri na kama shi Walid ɗin ba ba, kar shi ma ya zille mini, kuma an tabattar mini da ɗan amanrsa ne, ina dai  ta bibiyar su ta hanyar mai unguwa, da wasu daga mutanen unguwa. Wanda nake baki labarin nan ma ɗan mama, ya daina zuwa arear da aka gaya mini kai kayan shaye-shayen na su, abun ne dai duk sai a hankali". Tayi ajiyar zuciya ta ce "Wani aiki sai mai shi, Allah dai ya ba da sa'a, sannu da ƙoƙari DSP" "Yauwwa arfan Abba, bari na tafi" "To yanzu can ɗin zaka tafi?" "Eh, zan je in sake zaɓar yarana su shiga unguwar su madakin a farin kaya" Ta ce "Shikenan, a sauka lafiya, Allah ya tsare" ya amsa da Amin, ya nufi motarsa. Cikin sassarfa, ta nufi ɗakinta, Wayar Viper taƙi shiga, ta din ga kira amma a kashe. Hankalinta ya ƙara mummunan tashi, har la'asar wayar viper ba ta shiga. Shiryawa tayi ta saka niƙab, ta lallaɓa ta fice, ba tare da yi wa kowa sallama ba. Sauri take yi tamkar za ta tashi sama haka take fafaka sauri. A hanya aka fara kiraye-kirayen sallar la'asar, har ta ƙarasa kiran lambarsa take yi, amma shiru bai ɗaga ba. Ɗan mama ta tarar a tsakar gida, shikaɗai, yana ta shafawa wuƙaƙe wani abu, da ba ta san ko mene ne b. Ya miƙe yana kallonta ya ce "Dan Allah suna ina?" "Su wa?" "Su viper, da sauran". Ɗan mama ya ce "Oga Viper ya fita, ya tafi cikin gari wurin madaki, da shi da Oga liti, Oga walid sun yi faɗa ya fita" Jikinta na rawa ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, shi Walid ɗin ina ya tafi? Wai ma meyasa Vipern ne yake da taurin kan tsiya, akwai hatsari a hakan fa " "Ke, Oga Vipern ki ke faɗar baƙar magana a kan shi?" Ta juya zata fita ya ce "Ina zaki?" "Bin sa zan yi" Ya waro ido ya ce "Ina?" Ta tsaya ta kalleshi ta ce "Dabar madakin, ai na san wurin" zai yi magana, ta fita da sauri sosai. Shida saura na yamma, ta isa unguwar su madaki, saboda azalzalar da ta din ga yi wa mai adaidaita sahun da ta hau. Ta cikin niƙabinta, take kallon unguwar, ba zata taɓa manta, yadda aka sakar mata karnuka ba, suka kusa cinyeta. Ta nufi cikin unguwar, sai dai kamar babu mutane, sai ɗaiɗaikun mutane da suke guje-guje. Ta tsaya tana neman wand zata tambaya meyake faruwa, amma kusan kowa ta kansa yake yi. "Kai ku tafi gida, wannan ɗan tijarar ne ya shigo neman masifa, mai zamani ne da yaransa, suke faɗa da yaran madaki" taji muryar wani matashi, yana yi wa wasu yara magana" maimakon ta tsorata sai ta kutsa kai ta cigaba da tafiya tana fatan Ubangiji Allah ya sa kar wani abu ya same shi, Allah ya sa ta ganshi. Tana saka kai wani layi, ta ga an yanki wani a cinyarsa, jini ya yi tsartuwa, ta gigice cikin tashin hankali ta fara ihu, ji tayi an ja hannunta da ƙarfi, an shiga da ita wani layi daban. Ayshercool 0808012143 54 Cikin matsanancin tsoro, ta rintse idanunta, zuciyarta na bugawa da sauri sosai. Da kyar ta iya buɗe ido ta ga wanda ya ja ta, kallo ɗaya ta yi wa idanunsa ta cire nata, saboda mugun kallon da yake yi mata. "Uban me ya kawo ki nan?" Mamaki take yi, yaya aka yi ya ganeta da niƙab. "Ba magana nake yi miki ba?" Ta ɗaga kai ta kalleshi ta ce "Haka muka yi da kai? Meyasa zaka fito, kana da tabbacin idan suka kamaka a wannan karon zasu barka da rai ne, ba fa za su yadda su sake wannan kuskuren ba, dan Allah kar ka ɓata mini aiki, dan Allah ka daina fitowa" mayafin da ya rufe fuskarsa da shi, ya sake gyarawa, ya sake damƙar hannunta, ya din ga ratsa hanya da ita, kowa ya gudu gida ya ɓuya. A haka suka ƙaraso titi ya ɗaga wa wani mai baburin adaidaita sahu hannu, ya yi mata nuni ta shiga, shi ma ya shiga. Ta kalli yadda duhun magariba yayi, sai a lokacin hankalinta ya kai kan me za ta ce a gida. Ya ciro wayarsa, ya danna wata lamba, ya saka a kunnensa, a hankali yake magana ba ta iya jin me yake cewa a wayar,  ya zirawa mai napep ɗin dubu ɗaya ya kama ƙarfen adaidaita sahun, ya dire ba tare da mai napep ɗin ya tsaya ba. Cikin sauri ta leƙa, ta ga wani ya tsaya a babur sanye da face mask, Viper ya hau suka yi wani wurin. Tana jin yadda wayarta take ta ringing, amma taƙi ko ɗaukkota, balle ta ga waye. Ta gaya wa mai napep in da zai kaita, tuni aka fara kiraye-kirayen sallar isha'ai, motar Abba ta tarar da ta Nasir, alamar duk suna gida, gabanta ya faɗi. Sannu a hankali ta ƙarasa falon, ta tarar da Abba a tsaye, hannunsa riƙe da waya, take wayarta ta hau vibrating alamar ita yake kira a waya. Yayi mta wani irin kallo, da sai da hantar cikinta ta kaɗa. "Daga ina ki ke?" Tayi tsuru-tsuru da ido, tana kallonsa. Nasir ya ce "Magana fa ake yi miki" "Amm, Abba dama wallahi wata shaida nake so na haɗu da ita, wani case ne a hannuna shiyasa na fita". Abba ya ce "Wa ki ka gaya wa zaki fita?" Mama ta ce "Yaushe za ta gaya mana, tun da bamu isa ba" "Wato arfa kullum rashin jinki ƙara gaba yake yi ko? Idan baki yi wasa ba, hatta aikin sai na hana ki zuwa, an ce tun safe ba kya gidan nan, wace irin shaida ce haka?" Nasir ya ce "A'a har azahar tana nan ina ga da la'asar ta fita" "Koma menene yanzu yakamata ta shigo gida, ƙarfe takwas da wani abu tun la'asar?" Ta sunkuyar da kai ta ce "Dan Allah Abba ka yi haƙuri, in sha Allah ba zan sake ba" "Daga yau, ki ka sake fita babu wanda ya sani, zamu gauraya da ke" ta jinjina masa kai, ta wuce tana yi wa Allah godiya, da bai yi mata faɗa sosai ba. Addu'a ta din ga yi, Allah ya sa kar Viper ya aikata wani abu da za a kama shi, ko kuma ya yi wa kansa illa. Gashi ba ta samu sun yi magana a kan abun da ya kaita ba, na shirin da Nasir yake yi na son kama shi ta hanyar Walid ba. Madaki ne a tsaye yana kallon Al'amin da yake tsaye a gabansa, duk da duhun dare ne, amma manyan fitilun solar sun haske ko ina da ina. Idon Al'amin kamar ana hura wuta, Madaki yayi dariya ya ce "Mahadi mai dogon zamani, ka ci na wasu gaka kana cin naka. Viper ka ke maciji mai hatsarin gaske, dodon cinnaku masu ƙaryar kaki. Barka da sake haɗuwa da kai a dai-dai wannan lokaci, bayan dogon lokaci bamu yi ido da ido. Tabbas labarin Mai zamani ba zai taɓa cika ba, sai an ambaci madaki. Maza gumbar dutse ya ake ciki ne?" Yana rufe bakinsa, Al'amin ya soka masa russia a cinyarsa, a take jini ya fara kwarara a jikin madaki. Madaki ya kalli cinyarsa, ya kalli Al'amin. Al'amin ya kalli madaki ya ce "Na san zaka yi mamakin, yaushe na samu makarin tsafinka, amma na ƙyaleka a raye kana cin karenka babu babbaka. Yadda daba ta bar mini mugun tabo a zuciyata, ka rubuta ka ajiye, kamar yadda ka ce labarin Viper ba zai cika ba, sai an ambaci sunanka. Ina mai tabbatar maka Viper zai yi maka saran da bai taɓa yi wa wani irinsa ba. Kamar yadda ka canje ni, ka ke yi wa Indabo aiki, a madadina, ina da saƙon da zan baka ka bashi. Ka gaya masa ya toshe dukkanin ramukan da ke gidansa, ofishin sa da duk wani wuri da yake zuwa, saboda maciji ba ya raina ƙofa komai ƙanƙantarta, kuma ya tsammace ni, ta in da bai taɓa zata ba, kuma lokacin da bai taɓa zato ba. Al'amin na rufe bakinsa, madaki ya saka masa ƙarfe a damtsensa, a take kokawa ta kaure a tsakanin su, sai dai madaki ya kasa sarrafa ƙafar da Viper ya soka masa wuƙa, rabon da a zubar masa da jini har ya manta, saboda laƙanin taurin da yake amfani da shi, fitar masa da jinin da Al'amin yayi, yana nufin laƙanin ya karye, kuma a kowane lokaci, ana iya yi masa rauni da ƙarfe koma a kashe shi. Sosai suka din ga yi wa junansu illa da makami, sai dai Madaki ya fara galabaita, dan haka ya fara ƙoƙarin guduwa, dan ba ya son wasu su farga cewar ƙarfe ya fara tasiri a jikinsa. Amma Viper ya hana shi yin hakan, zuciyarsa ta din ga wata irin tafasa, ya din ga saran madaki, madaki ya saka hannu ya shaƙe Viper, take Viper ya ji abun da ya taɓa ji idan madaki ya shaƙe shi, tamkar an yi masa sarƙa da dutse, ya kasa motsi. Viper ya ji an saka masa wani abu a gefen wuyansa, a take ya silale ya ya faɗi ƙasa. Madaki ya ja da baya yana kallon yadd mutumin ya saita shi da bingida, dan bai ga ta in da ya ɓullo ba. "Zaka iya tafiya" mutumin yayi magana yana nuna masa hanya. Madaki ya ja jiki da kyar, yana ɗingisa ƙafa ya bar wurin. Wasu mutane manya manya majiya ƙarfi suka ɓullo wurin "Yaya kun tarwatsa yaran?" "Eh sir, amma fa har an sanar da 'yan sanda zancen rikicin sun taho" "Maza maza ku ɗauke shi ku tafi da shi, ayi masa treatment, ayi sedating ɗin sa, har a gama yi masa komai, kar ku mayar da shi maɓoyarsa yanzu, a bari zuwa da safe, idan yaransa sun fita nemansa sai ku mayar da shi. Su kuma su musa su tabattar sun goge duk wani trace da zai sanya a gane yazo unguwar nan" "Ok sir" Suka cicciɓi Al'amin, suka saka shi a mota, suka ɗauki wuƙarsa da wayarsa, suka tafi. Har wajen goma na dare, Nabila tana kiran wayar Viper, amma ba ya ɗagawa, hankalinta ya fara tashi, ko wani abu ne ya same shi, amma sai ta tuna, kaɗan da aikinsa ya ƙi ɗagawa mussaman ma da tayi masa laifi yau. Liti kuwa bayan ƙura ta lafa, ya koma gida, sai dai bai tarar da Viper ba, sai Walid. "Wai Viper bai dawo ba?" Yayi maganar yana kallon Walid. Walid yayi masa banza. "Malam magana nake yi maka fa" "Ban sani ba, da ni kuka fita?" Liti yayi tsaki ya ce "Bari na san yana hanya shi da ɗan mama" Walid ya ce "Ina fatan kun kashe madaki, kun wuce kun kashe Indabo" "Ban sani ba" Walid ya girgiza kai, ya cigaba da abun da yake yi. Ɗan mama ya shigo shi ma, jikinsa duk jini da alama yayi ɓarna sosai, ya ce "Oga liti ina Vipern, ina fatan yana lafiya, ni fa tun da muka afkawa su lakwari, ban sake ganinsa ba" Liti ya tashi tsaye ya ce "Kamar yaya? Ya haɗu da madakin ne?" "Ai ban sani ba, da muka rabu da ku, wani wurin yayi ai" "Bari mu jira nan da awa ɗaya mu gani" Walid ya ce "Hmm" "To yana nan lafiya, ai ba wani abun ne ya same shi ba" Walid ya ce "Na yi maka magana ne?" "To kama yi mana" Walid ya ce "Wallahi wani abun ya same shi, sai ranka ya ɓaci liti, daga kai har ɗan mama muguwar kasada cw da ganganci abun da ku ka biye masa ku ka yi. Kuma tun da ya kai i yanzu, akwai abun da yake faruwa gara kawai" yayi maganar yana miƙewa tsaye, ya ɗauki wuƙa ya soke a jikinsa, ya fice. "Ɗan mama, Walid fa gaskiya ya faɗa anya ba wani abun ne ya faru ba?" "Tashi mu koma, akwai matsala mun yi wauta da muka bar shi ya yi mana wayo, da ƙyar idan bai haɗu da madaki ba" haka suma suka tashi, suka fita. DSP Nasir da kansa ya jagoranci tafiya unguwar su madaki, bayan kiran da suka samu daga mai unguwa, sai dai da suka je ba su tarar da kowa ba. Duk ga alamu nan na faɗan dabar an yi, dan 'yan unguwar sun tabattar da hakan. Da safe Nabila har ta gama shirinta, baya ɗaga wayarta, tana zaune tana karyawa, ta shiga what's app tana duba messages, sai ga wani saƙo, an turo mata wani voice message, amma bayan an turo lambar tayi blocking ɗin ta. "Dan Allah ku taimaka mini, a ƙwato mini hakkina, an yi wa ɗiyata fyaɗe, na nemi a bini hakkinmu a kotu, amma wata Naja'atu Bunkure ta ce mana ita lawyer ce, ta ce zata taimake mu, amma wai sai mun janye ƙorafinmu, ko mu haƙura wanda yayi laifin yafi ƙarfinmu. Tayi mana tayin kuɗi bamu karɓa ba, yaron ya zo har gida, ya ci mini mutunci, ya ɗauke mini ramma ya tafi da ita ta ƙarfin tsiya, ban san ina ya kai mini 'ya ba, ya dawo ya karɓi kayanta, wai nayi haƙuri ta zama tasa. Ban san meyake nufi ba, dan girman Allah a bi mini hakkina, a nemo mini 'ya ta bani da ƙarfin ja da su, ni talaka ce, amma dan Allah a dawo mini da 'ya ta mu ji da ciwo ɗaya na keta mata haddi da yayi, ku taimaka mini dan Allah" matar ta ƙarasa maganar tana kuka. Da sauri Nabila ta tashi tsaye, ta din ga kunna voice ɗin tana saurare, wani irin gumi ya fara tsatstsafo mata, ba ta raba ɗaya biyu, wannan Muryar babar ramma ce, ita ce Muryar da aka saka a radion su Sumayya. "To amma waye ya turo mata voice ɗin?" Ta tambayi kanta. Buɗe ƙofar office ɗin da aka yi ne, ya sanya ta ɗan nutsu. Mutumin nan ne da yake zuwa wurin Barrister kabir, babban mutum ne sosai. "Na shigo ko na koma a nema mini iso?" Ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Bisimillah" Ya shigo ya zauna, ta ɗan risuna ta ce "Sannu da zuwa sir". "Yauwwa barrister Nabila, ya kike ya aiki?" "Alhamdilillah" Ya ce "Masha Allah, ai na yi wa Kabir magana, shi ya bani numbernki, kuma na kira kin ce sai na zo office" ta waro ido ta ce "Dama kai ne? Yi haƙuri dan Allah, ban sani ba na zata kawai masu haɗa lamba ne" Yayi murmushi ya ce "Kar ki damu, hakan yana da kyau ai, ai mace da aji aka santa. Sunana Wada M karofi, maybe kina ɗan jin sunana" Tayi murmushi ta ce "Oh yes, dama kai ne M karofi?" Ya jinjina mata kai ya ce "Eh barrister, ina son ki zama ɗaya daga cikin lawyoyina, masu kula mini da dukiyata da kadarorina, ina biya sosai, na yaba da nutsuwarki, na ce da ganinki zaki yi amana, na yi magana da barrister Kabir ya ƙara bani tabbacin hakan". Nabila ta gyaɗa kai ta ce "Haka ne, amma am very sorry sir, ni bana son irin wannan, a bar ni a hakana kawai" Yayi murmushi ya ce "A bar ki a hakanki anya kuwa? To shikenan idan ba za a kula da dukiyata ba, to ni a kula da ni mana" yayi maganar yana kallon ta. Murmushi ta yi tana girgiza kai ta ce "Haba sir, manya ba sa haka fa" "Subhanallah, na yi miki tsufa kenan?" "A'a ban ce ba, namiji ai baya tsufa" "To shikenan, zamu yi waya, bari na barki ki yi aikinki, idan ta kama ma sai na zo gida" "To Allah ya kawo ka lafiya ya tsare" "Amin Barrister na, ga wannan ki sha ruwan roba, ba na leda ba" yayi maganar yana ajiye mata kuɗi a kan tebur" "Ina fatan ba cin hanci ka bani ba, hakan ba zai hana in ta kama na saka alƙali ya ɗaure mini kai ba"ta yi maganar tana kallonsa. Ya yi dariya ya ce "Funny you, ni na isa, ayi aiki lafiya" ya fita yana murmushi. Yana fita ta ɗauki kuɗin ta ce "Alhamdilillah, tsuntsu daga sama gasashe, Allah ya kawo amanar baban wasu hannuna, na samu mai zuba mini mai idan mota ta iso" da sauri ta zube kuɗin, ta sake ɗaukar wayarta, ta sake jin voice message ɗin nan, tayi sauri tayi saving ɗin sa a gmail ɗin ta, dan kar ya ɓata. Kamar ta turawa Sumayya, sai kuma ta fasa. *** Ramma na kan dining tana karyawa, ta jingine waya tana kallon Abdul da shi ma karyawa yake yi. "Rahama kin taɓa gaishe ni kuwa?" "Waye ɗi na kai da zan gaisheka?" "Your life saver mana, yadda na ceci rayuwarki, da ki ka kusa mutuwa" "A'a da ka sha giya dai ka kusa kashe ni" Ya sosa kansa ya ce "Ke abu ba ya wucewa ne, sorry mana" Ta harare shi ta ce "An ƙi ayi sorryn" Ya kashingiɗa ya ce "Ɗan cire hannunki, na din ga gani sosai" Cikin rashin fahimta ta ce "Ka ga me?" Ya ɗaga girarsa yana nuna mata ƙirjinta. "Wallahi Abdul ka ɗuma asara, kai a duniya abu ɗaya Allah ya saka maka a cikin kanka ne? Haba mana" "Future governor ki ke gaya wa haka? Zan fa hanaki first lady, kodayeke wadda zan aura ce zata zama first lady, ke kuma maid ɗin ta" tayi shiru, tana tauna cornflakes. "Ki lallaɓa ni na dawo da wuri" A fusace ta ce "Kar Allah ya sa ka dawo ɗin, in sha Allah ka tafi kenan, ko jirgin ya faɗi, kai kaɗai ka mutu" Yayi dariya ya ce "Kin ga sai ki mutu kekaɗai a gidan nan ba, dan babu wanda ya san na ajiye ki a ciki. Gara ki yi sauri ki janye addu'ar ki, idan kina son ki fita" Ajiye kofin tayi, ta fashe da kuka, har da sheshsheƙa. Ya ce "Is ok, ke ce ba ayi miki abu, sai ki yi ta tsine mini, ina jin pain fa, am sorry ya isa haka, haba your excellency" maimakon ta yi shiru, sai ma ta ƙara sautin kukan, nan da nan ya rikice, ya hau bata haƙuri, amma tayi disconnecting kiran, ta cigaba da kuka. Ta ɗauki wayar, tun da ya tafi, take gwada kiran lambobi daban-daban, amma ba ta tafiya sai ta sa kawai. Ta dudduba ko ina, ko da hanyar da za ta iya guduwa, amma babu ga wata irin kewar mama da sani ƙaninta da take yi. Su liti tamkar za su yi hauka, gaba ɗaya suka rikice, da Viper bai kwana a gida ba, duk in da suke tunanin za su ganshi ba su same shi ba. Har gidansa Walid ya je, ya haura ta katanga, ya shiga amma ba su same shi ba, gashi madakin da aka ce ya zo yana unguwar, shi ma yayi ɓatan dabo, an neme shi an rasa. Gaba ɗaya hankalinsu ya tashi, mussaman liti, amma saboda tsananin ƙi faɗi, yaƙi yarda ya karɓi laifin, Walid ya din ga yi musu luguden ashariya daga shi har ɗan mama, suka yi masa shiru suka ƙi kula shi. A sukwane Nabila ta tashi daga wurin aiki, bayan cin karo da batun faɗan daba a tsakanin yaran madaki da na Viper, sai dai babu ɗaya daga cikin su da ya zo hannu, tsakanin Viper da madaki, al'ummar unguwar na cigaba da zaman ɗar-ɗar, sakamon rashin tsaro. Ofishin Nasir ta tafi, babu sanarwa sai ganinta yayi, sai da hankalinsa ya tashi ya ce "Arfa lafiya kuwa?" Ta ciro wayarta ta nuna masa posting ɗin. Ya ce "To wannan ne ya saka ki ka taho har nan?" Ta ce "Eh, na yi zaton baka sani bane" Ya girgiza kai ya ce 'No, na sani" "To yaya ake ciki?" Ya ɗan tsareta da idanunsa sannan ya ce "Ni duk kin ruɗa ni, ko kece ke binciken nan, sai haka Arfa. Na je, sun yi faɗan daba, amma babu tabbacin yazo". "Baka kama shi ba kenan?" Ya jinjina mata kai alamar eh. "To ko yaran nasa ba ka kama ba?" "Lokacin da muka je, sun yi sun watse" wata irin ɓoyayyiyar ajiyar zuciya ta yi, sannan ta ce "To shikenan, ai ban zaci ka gani ba, shiyasa na zo da kaina, bari na tafi" Nasir ya ce "Yanzu mussman ki ka baro aikinki ki ka zo kawo mini rahoto, arfa mai abun mamaki, zauna na gama abun da nake yi, na rage miki hanya" Ta ce "A'a yi aikinka, ina da wurin zuwa" ta lallaɓa shi ta fice. Sai dai hankalinta ya rarrabu kashi-kashi, voice ɗin nan da aka turo mata, babbar shaida ce da zata shiga kotu da ita da ƙwarin gwiwar ta. Abdul ya kira saif a waya, ya tambaye shi yaya ake ciki ya ce masa "Wallahi Abdul babu labarin matar nan, duk wani bincike da yakamata na yi na yi, amma shiru babu labari". "Lahaula wala ƙuwwata illa billa, Saif akwai matsala me zan ce wa yarinyar nan idan ta gano mahaifiyarta tayi ɓatan dabo, bayan babu irin magiyar da ba ta yi mini ba, a kan na mayar da ita" "To wannan kuma kai ta matsewa, tuntuni da ka san abun yi a kanta da duk ba a kawo nan ba" Abdul ya ce "Dole na gano in da mahaifiyar rayya take, idan ba haka ban san kalar tsinuwar da za ta yi mini ba" Saif ya ce "Ban gane tsinuwa ba, tsine maka take yi?" "Manta kawai" ya kashe wayar, ya din ga kiran wayar ramma, saboda tun jiya da safe da tayi kukan nan, ba ta sake ɗaga wayarsa ba, hankalinsa yayi mummunan tashi, ya fara tunanin ko wani abun ne ya sameta, kar ya je ta yi wa kanta illa, dan da wuƙaƙe a kitchen, kuma tana yawan iƙirarin cewa zata kashe kanta. Kusan awanni ashirin da huɗu suka shuɗe, Nabila ba ta samu Viper a waya ba, can ɓangaren su Walid ma, hankalinsu ya kasa kwanciya, saboda yawon neman Viper. Har ta je wurin aiki, ta kasa sukuni, kawai ta yanke shawarar zuwa gidan da yake. Tana sauka daga abun hawa, wata mota ƙirar helux baƙa, ta fito daga hanyar, duk da wurin mota ba ta iya bi, tayi ta tunanin yaya aka yi mota ta bi ta wurin, ta ƙarasa gidan, tun a tsakar gida take sallama, amma shiru babu wanda ya amsa, ta nufi ɗakinsa, ta ganshi a kwance a kan katifa, gefensa ga wuƙarsa da wayarsa da ledar magunguna, yana sanye da riga baƙa armless, da dogon wando shi ma baƙi, ga damtsensa an yi masa ɗinkin rauni, da sauran wurare a jikinsa. Cikin hanzari ta ƙarasa tana faɗin "Subhanallah" "Viper meyasameka?" Sai dai kamar gawa, ta ƙare masa kallo, an yi masa askin uwar sumar da take kansa, an yi masa gyaran fuska tare da rage masa gashin da ya taru a fuskar sa. Yayi wani irin ƙayataccen kyau, hatta kayan jikinsa ba ƙaramin kyau suka yi masa ba. Wayarta ta ciro ta din ga ɗaukarsa a hoto. Ta daddaki gefen katifarsa ta ce "Viper, bacci kake yi ne? Garin yaya ka ji raunuka haka?" Sai dai shiru ko motsi baya yi. "Me ka sha har haka ne? Ko sai na ce Master zaka tashi?" Babu tsammani ta ga yana motsawa a hankali. "Madarata" Nabila ta ce "Too yau kuma?" Yayi murmushi idanunsa a lumshe ya ce "Ai a duniya babu wanda ya raina ni, daga ke sai Walid, kin daina jin tsorona gaba ɗaya zan kama ki ne" murmushi yake yi sosai, wanda hakan ya bayyanar da tsantsar shauƙi da soyayyar da yake yi mata. Surutansa ya cigaba da yi ya ce "Yakamata na gaya miki wani abu, da yakamata ace kin sani, amma sai kin haihu tukuna, saura kuma ki isheni da tambaya na san halinki" ya buɗe idonsa a hankali, ya kalli Nabila da ta zuba masa ido, ya miƙa hannunsa ya riƙo nata ya ce "Zan gaya miki me na je yi Lagos ne" sai kuma ya saki hannunta yana girgiza kai. "Laaa, ke ya aka yi ki ka dawo da shi, Walid ƙaraso ka ga" liti yayi maganar yana shigowa ɗakin. Gaba ɗaya su ukun suka shigo, suka kewaye ta. "Da gidan uban wa ki ka kai shi?" Ta kalli Liti ta ce "Kamar yaya?" "Gidan uban wa ki ka kai shi?" A ƙule ta ce "Gidan ubana, tayaya zan iya ɗaga wannan shirgegen ƙaton" "Ƙarya ki ke yi haɗa baki aka yi da ke aka ɗauke shi, wannan kayan na jikinsa ma ba nasa bane ba macuciya" Walid ya ce "Ya isa dan Allah, Barrister nemansa muke ko sama ko ƙasa bamu ganshi ba, a ina ki ka gano shi?" Ta ce "Wallahi yanzu na zo, bana samunsa a waya, yanzu na zo kawai na tarar da shi a kwance, wallahi ban san ma neman sa ku ke yi ba, duba wayarsa zaka missed calls ɗina da yawa. Amma dai naga wata baƙar helux ta fita daga hanyar nan, ban san ta ina suka biyo ba, na riƙe lambar motar a kaina" Walid ya ce "Karki damu, na yadda da ke" "Wallahi mai laya, ka cigaba da sakankancewa da yarinyar nan, sai tayi dalilin an kashe ku tukuna" Liti ya ƙarasa gaban Viper ya durƙusa a kansa, cikin zafin nama, viper ya danƙi wuƙarsa ya saita ta a cikin liti yana wani irin huci. Liti ya buɗe baki ya ce "Ni zaka sa wa russia Viper?" A hankali ya ƙara buɗe idonsa, ya hankaɗe liti gefe ya ce "Na zata madaki ne" sai kuma ya kalli jikinsa, ya kalli kayansa, ya kalli damtsensa ya ga ɗinki, ya kalli Nabila ya kalli ɗakin ya ce "Ke a ina muka rabu da ke?" Ta ce "A titi, bayan ka dire daga adaidaita sahu". "Me ki ka yi mini?" Nabila ta ce "Au kaima ni ka ke zargin na sace ka kenan?" Walid ne ya yi masa bayanin abun da ya faru, ya lalubi wayarsa da sauri yana duddubawa. "Don't endanger your life again, madaki is still not your mate, da sauran lokaci" ya ajiye wayar ya sunkuyar da kansa, da yayi masa nauyi yana tuno abun da ya faru a ranar. Nabila ta kalli Walid ta ce "Yay walid, yayana yana zuwa wurin sayar da shayinku, kuma akwai jami'ansa a farin kaya suna zuwa, kayi taka tsantsan, yanzu aikinsa a kanka yake. Kuma ka kula da wanda suke zuwa wurin sosai, kar wani information yayi leaking a wurin" Liti ya ce "Munafuka, wadda take kwarewa ɗan uwanta baya ne, ku ke tunanin kuma ba zata bar ku ba wataran. Shegen yayan naki azzalumi, ƙugu kamar gatari" Nabila ta ce "Allah ya isan sa, kuma ni ba munafuka ba ce, kuma wallahi idan baka kiyayeni ba, zan kuma sakawa a kama mini kai, sai igiya tayi saura" tayi maganar tana hararsa ta ɗauki jakarta. Ta durƙusa a gefen Viper ta kai bakinta, kunnensa ta ce "Viper, zan tafi zan je wani wuri, zamu yi waya, ka samu ka ci abinci, kar ka takurawa kanka da tunani da yawa, kar ka sha ƙwayoyin da za su yi maka illa. Saboda muna son ganinka cikin ƙoshin lafiya da ni da 'yar madara, na ji ka ce zaka gaya mata wani abu, to nima sai ka gaya mini, tun da nice amarya. Kayan nan sun yi maka kyau sosai da sosai, ka ci abinci kayi salla ka huta, ka bar wayarka a buɗe zamu yi magana dan Allah, ka yi mini addu'a zan cigaba da shari'a da su bunkure, take care dear" ya ɗaga kai ya kalleta, taƙi kallonsa tayi waje. Liti ya ce "Makira, duk makircinki sai ya koma kanki". Ta galla masa harara ta tafi. *** Abdul yana ta kiran ramma, har ya fitar da ran zata ɗaga, yaji ta ɗaga muryarta ƙasa-ƙasa. "Bacci ki ke yi ne?" Ta ce "Eh" "Eyya sorry na tashe ki, nake ta kiranki a waya amma ba kya ɗagawa, lafiya dai ko?" "Haushinka nake ji ne, zan iya ɗuɗɗura maka ashar, shiyasa bana ɗagawa" Yayi dariya ya ce "Yanzu kin huce?" "Eh" "To masha Allah, kin tashi lafiya?" "Eh" "Duk muryarki wani iri, anya lafiya kuwa?" Ramma ta ce "Ba wani lafiya, ni na gaji da zaman gidan, nikaɗai kamar mayya sai tv da haushin karnuka, ni ba prisoner ba". Abdul ya ce "To yanzu ya ki ke so ayi?" "Ni koma yane ayi" Ya ce "To shikenan, zan dawo gobe in Allah ya kaimu" "Ba sati ka ce zaka yi ba?" Ya ce "A'a hankalina yaƙi kwanciya ne, zan dawo gobe in Allah ya kaimu " Ramma ta ce "To Allah ya tsare" "Kin fasa in faɗi a jirgin, kar in dawo?" "A'a jirgin ya faɗi kai kaɗai ka mutu" "Muguwa ba Amin ba" "Ban kai ka mugunta ba ai" Yayi dariya ya ce "Sai anjima". *** Washegari ya kama ranar da Nabila zasu cigaba da shari'ar mai gadi, ta shiga office ɗin ta, ta tarar da wani file a ajiye a kan teburinta, har ta fara masifar na meye wannan aka ajiye mata a kan tebur. Ta nemi wuri ta zauna, ta ɗauki wayarta, ta shiga social media ta rubuta, kuraye masu fatar akuya, an kusa walƙiyya mu ga kowa" ta yi tagging ɗin Naja bunkure.Washegari ya kama ranar da Nabila zasu cigaba da shari'ar mai gadi, ta shiga office ɗin ta, ta tarar da wani file a ajiye a kan teburinta, har ta fara masifar na meye wannan aka ajiye mata a kan tebur. Ta nemi wuri ta zauna, ta ɗauki wayarta, ta shiga social media ta rubuta, kuraye masu fatar akuya, an kusa walƙiyya mu ga kowa" ta yi tagging ɗin Naja bunkure. M karofi ya kirata, ya din ga yi mata surutu, da neman ta bashi damar zuwa gidansu, ta ce masa yanzu aiki take yi, bayan sun yi sallama, ta ja file ɗin tana dubawa. Sunan Naja'atu Bunkure ne a sama, sannan aka fara bayanin tarihin rayuwarta tiryan-tiryan, har zuwa fara aikinta, yadda ta taso cikin rayuwar ƙunci da wahala, yadda ta zama lawyer, bayan fyaɗe da aka yi mata da ƙanan shekaru, gaɓar da Nabila ke son ganin meyafaru, a nan aka tsaya. Ta daki tebur, ta din ga jujjuya file ɗin tana tunanin waye wannan ya kawo mata file ɗin nan, da kyar idan ba shi da alaƙa da wanda ya tura mata voice message ɗin nan. *** DSP Nasir yana zaune yana rarraba ido a ƙaton falon, da ko ina sanyin A.C ne ke ratsa shi. Babu tsammani mutumin ya fito, ya samu wuri ya zauna, cikin girmamawa Nasir ya ce "Barka da wannan lokaci sir" "Yauwwa barka, DSP Nasir Yusuf maitama, ɗan uwan barrister Nabila Yusuf maitama" ya ɗago ya kalle shi. "Na san zaka yi mamakin kiran da nayi maka ko?" Nasir "Ƙwarai sir, na san ni dai babu wani abu da ya taɓa haɗa ni da kai, amma ka saka a nemo ni, kuma ga sunana ka kama, da na ƙanwata" Indabo ya gyara zamansa ya kalli Nasir ya ce "Nabila!" Cikin rashin fahimta ya ce "Me tayi?" Ayshercool 08081012143 55 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin rashin fahimta, Nasir ya ce "Amma Yallaɓai me tayi ne?" Indabo yayi murmushi ya ce "Bari mu ɗan ajiye batun ta a gefe. Aminu Viper, wanda aka fi sani da mai zamani a baya, kai ne incharge of bincike da ƙoƙarin kama shi haka ne?" Ya jinjina kai ya ce "Eh sir" "Na san kana fuskantar matsin lamba, daga wurin na sama da kai, a kan lallai ka kama Viper. Duk da abun mamaki ne, a baya yana tsare a prison lokaci guda yayi ɓatan dabo sama da shekara guda ana nemansa". Nasir ya ce "Haka ne sir" Indabo ya sassauta muryarsa ya ce "Akwai jiƙaƙƙiya tsakanina da Viper, wanda barazana ne ga siyasata da mutuncina. Saboda haka na yanke shawarar yin gaba da gaba da kai mu tattauna wataƙila kafi bawa aikin muhimmanci, tun da na samanka kawai nake gani, kai bamu taɓa haɗuwa ba, kuma Alhamdilillah sai na yi sara a kan gaɓa" ya ajiye masa wata jaka ya ce "Ga wannan ka sha mai, sannan akwai fuloti mai rai da lafiya a unguwar tudun yola da takardunsa a ciki, wannan zai zama wani ɗan hasafi, ko in ce ihsani domin ƙara maka ƙwarin gwiwa, idan aiki ya kammala, ina da kyakykyawan Albishir gareka, muddin Viper ya zo hannu, ko ma ya bar duniyar baki ɗaya ina da ƙarin Albishir gareka. Ɗana na shirin zama deputy governor a garin nan, zaɓe mai zuwa. Kuma ka san kujerar da nake kai, ka san ma'anarta. Zan iya yi maka alƙawarin zama CP na jihar nan, kai koma na yi maka babban muƙami a ƙasa. Akwai kyautar mota irin ta sanatoci, da gwamanti kan yi gwanjon su, gida ko fili sai wanda ka zaɓa. Kar ka yi dogon tunani, ba wai cin amanar ƙasa zaka yi ba, taimakon kai da kai ne, kai ma ka taimaki gobenka, idan ba haka ba, a haka zaka ƙare kana yi wa ƙasar da ba ta san muhimmancin ka ba bauta, ka gama babu wani allowance ɗin kirki ka ƙare rayuwarka a tagayyare" Nasir yayi shiru yana ajiyar zuciya. "Sai magana ta biyu, Nabila ƙanwarka, akwai wasu abubuwa muhummai a tattare da ita. Abu na farko na sanya rayuwarta a matsayin tarkon da zan kama Viper ba tare da ta sani ba, duk da hanyar tana tangarɗa, amma tabbas ina ƙoƙarin kama Viper ta hanyar ta, ko da kuwa hakan yana nufin salwantar da rayuwarta ne" Cikin mamaki da rashin fahimta ya ce "Kamar yaya?" "Kamar yadda nake gaya maka, ai ba ta hannunku kawai nake nemansa ba, dan haƙa ƙwazonka, da nemo Viper shi ne zai kuɓutar da rayuwarta, haka zalika ka taka mata burki a kan shari'ar da take yi, na son yin gaba da gaba da Naja'atu Bunkure, saboda yin hakan tamkar yin fito na fito da ni ne, idan ba haka ba, wallahi rayuwarta zata salwanta a banza, ba zan taɓa bari sunana ya ɓaci a banza ko asirina ya tonu ba" Nasir ya ce "Amma sir, dole sai an shigar da Nabila cikin wannan lamarin?" "Dole ne, muddin kana son rayuwarta, make her withdraw the case, ta fita daga shari'ar nan" Nasir yayi sassanyar ajiyar zuciya ya ce "Zan duba naga menene abun yi" Indabo ya ce "Yauwwa, a ƙoƙarta, zaku tafi da P.A ɗina, za ayi wa motarka full tank, ka sanya ido sosai a kan yarinyar nan" Nasir ya tashi ya ce "Thank you sir" Indabo yayi murmushi ya ce "In dai muna tare, ka din ga samun damrmaki kenan, ai ba a zama haka DSP" ya jinjina kai ya juya ya fita, kansa yana wani irin nauyi. *** Cikin hanzari Nabila ta fito daga office ɗin ta, ta kalli mai goge-goge ta ce "Baba, akwai wanda ya shiga office ɗina kafin na zo ne?" Ya ce "A'a, shara kawai na yi na goge miki, na fito" "Kai ka ajiye mini wani file a kan tebur?" Ya girgiza kai ya ce "A'a, ban tarar da komai ba da na goge teburin" ta jinjina masa kai ta koma, tana cigaba da mamakin waye haka?. Ta window ta leƙa taga zuwan barrister Habib, tayi sauri ta fita, a ƙofar office ɗin sa ya tarar da ita ya ce "Ya dai? Tara ko bashi, ki ka tsaya mini a ƙofar office" tayi murmushi ta ce "Babu ɗaya, nemanka nake yi ruwa a jallo ne" Ya saka mukulli ya buɗe, suka shiga, ya ce "Allah ya sa ba wata shirirtar ba ce? Nima ina nemanki dama" "Haba barrister, sai ka ce wata 'yar yarinya, is a very serious issue" Ya dubeta ya ce "To yanzu dai, ki yi haƙuri, na fara karyawa tukuna" Noƙe masa kafaɗa tayi, tare da girgiza kai. Ya ce "Ke, kwanan nan fa nayi mata ta biyu, da na sani ma da ke nayi ta biyun nan, wannan shagwaɓar taki ai sai ki hanani karyawa" "Taɓ matarka ta daka ni kenan, ni dai ka zauna Please muyi magana" Ya zauna ya ce "Na zauna Nabila menene?" Wayarta ta ciro ta kunna masa voice message ɗin nan, cikin mamaki ya kalleta ya ce "Waye ya turo miki?" Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, shiyasa na zo na nuna maka" "To ai tun jiya naso na kira ki, na je garinsu yarinyar da kaina, har gidan su na je, amma ban tarar da kowa ba, maƙwabta sun tabattar mini da ta shafe kwanaki ba su san in da take ba, kuma ba ta yi wa kowa sallama ba" Nabila tayi turus ta ce "Ban gane ba, uwar ta ɓata kenan? Ko kuma guduwa tayi saboda gudun abun kunya?" "Shi ne dai ban sani ba" Nabila ta ce "Na kasa gane kan lamarin nan, to waye ya turo mini voice ɗin nan, an ce shi wanda yayi mata fyaɗen, ya zo ya ɗauke ta, to ya aka yi da uwar, waye ya naɗi wannan recording ɗin?". Barrister Habib ya ce "Gaskiya dai abun tunani ne, lamarin akwai ɗaure kai, amma kar ki damu, koma waye sauƙaƙa miki aiki yayi" "Amma abun da mamaki fa, kuma wanda yayi hakan ba shi da wata manufa ta yin hakan, ya bayyana kansa mana idan yana da gaskiya koma waye" Barrister Habib ya jinjina kai ya ce "Yauwwa, ya ku ka yi da Alhaji wada M karofi?" Ta yamutsa baki ta ce "Soyaya muke yi " "Soyayya kuma? Cewa yayi yana son ki shiga cikin lawyoyinsa, masu kula da dukiyarsa fa" Ta ce "A'a gaskiya, ce masa nayi a'a, sai ya ce to shi na din ga kula da shi, shikenan" Habib ya ce "Innalillahi, wallahi baki da lissafi Nabila, kin san waye mutumin nan kuwa? Kin san kuɗin da muke samu a wurinsa kuwa? Babban mutum ne fa a ƙasar nan" Ta tashi ta ce "Oho, a hakan ma ai yana bani kuɗi, bana son dai ya zo gidanmu, naga he's very serious, kar ya zo suyi magana da Abba ace sai na aure shi, dan yasin bana son tsoho". Ya girgiza kai ya ce "Ƙuruci dangin hauka, Allah ya shiryeki" "Amin, ayi aiki lafiya" ta fice daga office ɗin. *** Ramma na zaune tana ta gyangyaɗi, ta ji ana murɗa ƙofar falon, Abdul ya shigo da akwatinsa. Suna haɗa ido ya sakar mata murmushi ya ce "I am back" murmushin ita ma tayi masa. Ya ƙarasa ya zauna tare da rungumeta, yayi kissing ɗin goshinta ya ce "Kina zaune baki yi bacci ba kina jirana?" "Ƙarfe tara fa ka ce, amma sai sha biyu, Club ka je ko?" "Wallahi ban je club ba, abubuwan da na tarar da yawa a can, Shiyasa na kuma samu matsala ne da flight ɗin shiyasa, gudowa fa nayi saboda ke" Tayi ajiyar zuciya ta ce "To sannu" "Yauwwa sweetheart " Ta ce "Taɓ babu daɗin ji" Ya ce "Wallahi da daɗi, rantse baki ji daɗi ba da na ce sweetheart" "Wallahi ban ji ba" Abdul ya ce "Ƙarya ki ke yi, santaleln mutum kamar ni, na kira ki da sweetheart, ki ce ba ki ji komai ba" "To waye kai ɗin? Sai ka ce wani mutum na musamman" Ya kaɗa ƙafa ya ce "Ke kin san matan da suke crushing ɗina kuwa?" "To ina ruwana?" "Kina da ruwa mana, na gaji fa sosai Saboda na san maybe kina nan kina jirana, ko abinci ban tsaya na saya ba, yanzu zan yi wanka, sai ki rakani mu duba in da suke 24hrs, mu ci abinci" Ramma ta ce "A'a, na yi girki ai tun magariba ma na gama, tun da nan gidan ba mak aiki, kayi wankan ka ci" Ya ce "Iyee zan ci jagwalgwalo yau, bari nayi wankan" ya ja akwatinsa, ya shiga bedroom ɗin da take. A falo ya tarar ta ajiye fulasai. "Rahama kayan miyan cikin fridge ɗin ba su lalace ba kenan?" Ta ce "Eh, har fruit ɗin, na iya reserving ɗin su ai" Yana cin abincin yana murmushi, ya ce "Yanzu har sakwara ki ka yi, gaskiya kina ji da ni, ga shayin ma yayi daɗi sosai" "Ba wani ji da kai da nake yi, tunani nake ina ma da guba a ciki, ka ci ka mutu" Yayi dariya ya ce "Koma dai menene, idan ma da gubar na ci, ba mutuwa zan yanzu ba, sai kin haifa mana babies, kuma fa zama zaki yi kiyi kuka idan na mutu. Anyway abinci yayi daɗi sosai, yaya aka yi ki ka iya girki haka?" Ramma ta ce "Aikina kenan a gidan Anty maijidda, ta ce ba ta taɓa yar aiki kamata ba, sai gashi iftila'i ya faru da ni a gidanta, amma ta kware mini baya, saboda kai ɗan ɗan uwnta ne, ni kuma bata da alaƙa da ni, ko ganin idonta ban yi ba, wai sai ma umarnin idan mun zo kar a bari mu shiga da ta bayar, aka canza masu gadi.shikenan bakomai, shi talaka ai Allah yana son abun sa" tayi maganar tana share hawayenta. Sai jikin Abdul yayi sanyi, ya ce "Rahama duk laifina ne, nayi kuskure, kuma duk sharrin giya ne da ruɗin shaiɗan, amma na rage shan giya ma, kuma wallahi rahama na daina bin mata, da ɗin ma sharrin giya ne da kuma abokai" tashi ta yi ta bar masa wurin, saboda tuno hanyar da ya bi ya ci mata zarafi da yayi. Shi ma gaba ɗaya sai jikinsa yayi sanyi, duk da irin zaluncin da yayi mata, tana da matuƙar tausayi da imani, duk da yana shan zagi da tsinuwa, amma wasu lokutan sauƙin hali ne da ita. A zaune ya tarar da ita a kan gado, tana ta uban kuka, bai ce mata uffan ba, ya rungumeta yana shafa bayanta, a hankali yake furta "Am very sorry for what i did, ki yi haƙuri" ya din ga rarrashinta, har suka kwanta, yana ta magana, amma tunani ne daban-daban a cikin kanta, babu tsammani ya ji ta ce "Abdul yasar" "Your excellency" "Wai dan Allah da gaske ana yi wa maza fyaɗe?" Ya ce "A'uzibillah, wannan wace irin magana ce?" "Shekarun baya, kan yayanmu ya mutu, kamar haka na so naji an ce, wani ne ya ce zai samo masa aiki a Abuja, shi ne yayi masa fyaɗe yayi rashin lafiya ya mutu, kullum mama ta tuno da shi, sai ta kusa kwana tana kuka, sai ta daina cin abinci, kusan shekara shida fa, amma ta kasa mantawa. Kuma dama ba a hannunta yake ba, shi yana wurin babansa a birni. To ni haryanzu ban taɓa jin an ce an yi wa namiji fyaɗe ba sai mace, shi ne nake tunanin, ko wani abun suke nufi daban ban gane ba". Dummm haka Abdul ya ji kansa yayi, ita kanta kalmar ga mace ma babu daɗin ji, balle ga namiji, sai yanzu ya ƙara tabattar da in dai zancen ramma gaskiya ne, ya zalunce su. Hakan ya saka ya ji dolensa ya ƙara ƙaimi, ya nemo mahaifiyarta, ya nemi afuwarta, amma bai ji a ransa zai iya mayar mata da ramma ba. "Abdul ka yi shiru, ka gaya mini mana" "Ke kin ga alamar in da za a yi wa namiji fyaɗe ne? To ban sani ba ko ana yi, tun da nima yaro ne haryanzu, ban sani ba ko ana yi" "Waye yaron?" "Ni mana" "Ka fiye abun haushi, da takaici, a'a mahaifa ne kai" murmushi ya yi yana sumbatar ta. *** "Mai zamani" Walid ya kira sunan Viper. Ya ɗaga ido yana kallon Walid. "Da gaske ka haɗu da madaki? Ko kuma yaransa ne suka yi maka wannan raunin na damtsenka? Na ji an ce an neme shi an rasa, kuma ban ji labarin yan sanda sun kama shi ba. Abun duk ya ɗaure mini kai, daga majiyarmu ta dabarsa, hatta su yaransa ba su san a inda yake ba. Kuma na san abu ne mawuyaci ku haɗu ace iya illar da yayi maka kenan, bai kashe ka ba, tun da ya san nemansa ka ke yi, kuma kai ma da ka kashe shi da an ji labari, kuma bana tunanin zaka iya kashe shi a yanzu". Viper ya gyaɗa kai, ya ɗaga russia da take hannunsa yake ta goge ta, yana shafa mata mai. Ya miƙawa Walid ita, ya karɓa. Ya ce "Meyafaru?" Al'amin ya ce "Duba da me aka ƙerata?" Mamaki ne ya kama Walid, tun da suke bai taɓa yi masa wannan tambayar ba, ya karɓa ya dudduba ta, ya ce "Ƙarfe ne" Viper ya ce "Duba dai" Ya sake dubawa ya ce "Ƙarfe ce Viper" Viper ya haɗa tafukan hannayensa biyu ya ɗaga ya ce "Allah ya jiƙan maza" Walid ma ya haɗa ya ɗaga ya ce "Amin, dodo babban sarki" Viper ya ce "Shi ya saka aka ƙera mini russia. An yi amfani da ƙashin ƙwaurin zaki ne, a samanta, ƙasanta kuma azurfa ce haɗe da ƙarfe, sai kuma aka yi amfani da magunguna wurin ƙarasa haɗa aikinta. Shiyasa ba ko yaushe nake amfani da ita ba. Ya saka an ƙera mini ita, ita ce makarin taurin da madaki yake amfani da shi. Sai dai a lokacin ban ji cewar ya dace na kawar da madaki farat ɗaya, na kashe shi ba, na cigaba da ajiyeta. A wannan karon naga yakamata na nu na wa madaki, talala kawai nayi masa. Saboda shi aka ƙera russia, na gwada aikinta ne a kansa, kuma tayi tasiri, dan kuwa ta huda shi, ya kuma zubar da jini. Ƙafar da na soka masa, ta tashi daga aiki har abada, ba zan kashe shi farat ɗaya ba, sai na gama sabauta rayuwarsa, Indabo ya watsar da shi a dalilin Rashin amfanin da ba zai yi masa ba. A lokacin da sauran waɗanda yake cuta, za su farga asirinsa ha karye ya daina tasiri, su ma su fara far masa da kai masa hari. A haka zan cigaba da yi wa gaɓoɓinsa yankan ƙauna, har sai na fara jin sanyi a zuciyata". Walid ya ce "Kan uba, yanzu duk tsawon lokacin nan, kana da makarin tsafin madaki, ka zauna muke bulayi? Har yayi maka illa ta biyu?" Ya sunkuyar da kai sannan ya ɗago ya ce "Tun a baya, nayi niyyar ɗaukar fansa, amma daga cikin alfarmar da matata ta nema a wurina, ya haɗa da na bar madaki da Allah, kar na kashe shi, ba ta son nayi kisan kai, sunana ya ƙara ɓaci, hatta gabarmu sai da ta roƙi na kawo ƙarshenta, idan ban manta ba, har Abbu ta sako a al'amrin. Kukanta ne ya tsaye mini a rai, tare da magiyarta, har na ji a raina na yadda, na haƙura zan kawo ƙarshen gabata da shi, domin in faranta mata amma.... Sai kuma yayi shiru, ya fara huci, jijiyoyin sa suka fara kumbura, gumi yana tsatstsafo masa a goshinsa. Walid cikin damuwa, ya daddaki kafaɗar Viper ya ce "Am sorry mai zamani, ka yi haƙuri, kayi haƙuri" *** Nabila na ta rubuce-rubuce a cikin system, ta jiyo muryar Abba yana "Ina Arfan Abban ne, ko ba ta dawo ba ne?" Daga ɗakin ta amsa ta ce "Ina nan Abba, gani nan" ta fito tana murmushi. Ya ɗago mata key, ya ce "To, ga 206 ɗin ki can an kawo, duk da na san ba kya son kalar motar" Wani irin tsalle tayi, ta rungume Abba, ta na "Subhanallah, wayyo daɗi ina zan saka kaina, Abba dama zaka sai mini motar? Na zata da wasa fa ka ke yi mini" murmushi ya yi, ya kama hannun ta, suka fita harabar gidan, wanda suka kawo motar ma ba su tafi ba, Vibe ce blue black sai sheƙi take yi. Kawai ta fashe da kuka, Abba ya ce "Ya kuka kuma?" "Abba na gode, na ma rasa me zan ce ne" 'yan gidan duk suka fito suna kallon motar, masu tayata murna nayi, masu tsaki suna yi. Ana haka Nasir ya shigo, ta nufe shi da sauri, tana nuna masa key ɗin motarta. "Congratulations, amma tawa zaki ɗauka ni bani sabuwar" Tayi dariya ta ce "Ai ba aro ba ɗani, balle kyauta" dama a karambani, Nabila ta iya mota, a kan ta Nasir, ya karɓi mukullin, walida ta ce bari ta zo a ɗana su, amma Nasir ya ce mata a'a, su biyu kawai za su fita. Suna tafe yana driving, bakinta yaƙi rufuwa. "Wow na zama big girl, idan zan je trial, sai dai a ganni a motata, a din ga cewa hajiya, shikenan na huta da hawa ɗan sahu, da masu warin hammata da zarnin fitsari" ya ƙare mata kallo, sai nishaɗi take yi tana murmushi. "Arfa" "Yes sir" "Ina son mu yi magana ne" Ta kalleshi ta ce "To yaya" "Shari'ar da ki ke yi, da kuma adawa da Naja'atu Bunkure" "Ok ina jinka" "You have to withdraw the trial" "What?" Nasir ya ce "For your own good and safety, mace ce mai hatsarin gaske, kar wani abu ya same ki, Abba ba zai iya jurewa ba, nima kuma haka ki rabu da matar nan" Nabila ta ce "Yaya, ni fa dama masu ƙaunata ba su da yawa a duniya, dan haka ka ƙyaleni, why would that innocent old man suffer just to cover someone's evil did, ita kuma ta din ga zaluntar mutane, kuma ayi mata shiri, i can't nima Allah ya tsaya mini". "Shut up, ina magana kina mayar mini, babu wanda ya shiga cikin maganar sai ke, tun da ki ga kowa baya tsoma baki a lamarinta, dan me ke zaki yi? Ki janye shri'ar nan tun ban saɓa miki ba, tun da baki san ciwon kanki ba. Ya zama dole ki janye, idan ba ƙafar wando ɗaya ki ke so mu saka da ke ba" ya haƙiƙance yana yi mata masifa. Tayi masa shiru, gaba ɗaya ta nemi farincikin da take ciki ta rasa, saboda maganar da Nasir yayi, ya gama zagayawa suka koma gida. Matan Abba kuwa mussaman mama, ta din ga mita a kan saya wa Nabila mota, itakaɗai a gidan, amma ya ce gidansa ne, abun da ya tsara shi za ayi, ba wanda aka tsara masa ba. Lokaci ne yayi da zasu girbi abun da suka shuka masa a kanta. Gaba ɗaya sai ta rasa karsashi, ta na ta zumuɗin kiran sumayya, amma yanzu ta kasa, saboda haushi da mamakin abun da Nasir yayi mata yanzu. Kawai sai ta kira Viper, ya ɗaga ya saka a kunnensa. "Ina wuni, ya jikinka kuwa?" "Alhamdilillah" sai da ta tashi tsaye jin ya amsa ta ce "Kai, yau ka amsa mini, masha Allah, Allah ya ƙara maka lafiya da nisan kwana, ya kare mana kai. Dama na kira ne in ji ya jikinka, kuma" sai tayi shiru, shima shirun yayi bai yi magana ba. "To ka tambayeni menene mana? Shikenan ma na san ba kulani zaka yi ba, sai anjima" ta kashe wayar ta ajiye, ta kwanta tayi shiru, zuciyarta a cunkushe babu daɗi, ga abun farinciki, amma Nasir ya ɓata mata. Kawai ta fashe da kuka, ta yi ta gama, ta kwanta ta hau bacci. *** Yau a kotu, hujjojin da Nabila ta bayar masu kyau ne sosai da sosai, sai dai lauyan gwamantin da yake kare ɓangaren ramma, sun fita gogewa suka din ga dankwafar da ita, kuma alƙalin ya din ga ɗaukar side, tare da soke wasu daga cikin hujjojin Nabila. Ya sake ɗaga shari'ar zuwa wata guda. Ta kalli dattijon, gaba ɗaya sai ta ji ta fara karaya. Jiki a sanyaye ta fito, tana fitowa murtala yana tsaye a harabar kotun yana jiranta. Kamar ta fashe da kuka ta ce "Yaya murtala kaga yadda shari'ar nan ke tafiya ko?" Murtala ya ce "Kar ki damu, ai idan sun san wata, ba su san wata ba, kamar yadda muka tsara zan tattauna da ke a kan shari'ar yanzu, ki faɗi hints mai muhimmanci, zamu saka a live program yau da ni da Sumayya, sai dai duk mai faruwa ta faru. Cikin damuwa ta ce "Kar fa ku samu matsala a wurin aiki" "Manta da su, duk da su ake haɗa baki ai, dattijon ne ma abun tausayi" Nabila ta ce "Wallahi ko kallonsa nayi, sai tausayinsa ya kama ni, bana son na kasa sakawa a wanke shi" Murtala ya ciro recorder ɗin sa, ya tattauna da Nabila, na mintuna biyar, a kan shari'ar sannan ya tafi. *** Indabo tamkar zai kwaɗawa Abdul mari, saboda takaici "Abdul wai me kake nufi da ni ne? Sai ka yi mini asarar wahalata, uwar me ka dawo kanon ka yi? Uban wa ka ajiye da ka taho, mutane sun zauna suna jiranka, kawai a nemeka a rasa, wane irin rashin mutunci ne, da iskanci har haka? Wato tona mini asiri zaka yi, ka nuna wa duniya ban isa da kai ba ko?" "Daddy, uzurin gaggawa ne ya taso mini, wata tiyat..... "Ubanka da kai da tiyatar, ko tunanin ɗan uwanka da yake mexixo a tsare baka yi, dole sai ka nuna mini ban isa da kai ba, ka cigaba kar ka fasa ka kuma kyauta" Wayar Abdul ta fara ringing, ya cirota ya ga lambar ramma, ya ɗaga a saka a kunnensa, yayi ƙasa da murya ya ce "Beb" "Abdul kana ina?" "Ina gida meyafaru?" "Tun jiya fa zazzaɓi nake yi, cikina sai ciwo yake ina amai" A rikice ya ce "Subhanallah, kina ji na, ki duba side bed drower, akwai pcm, ki ɗauka ki sha, daga shi kar ki sha komai, gani nan zuwa kin ji, ki samu ki kwanta" sai da ya kashe wayar, ya tashi tsaye, ya ankare da katoɓarar da yayi, gaba ɗaya ya manta a gaban wa yake. "Abdul karuwa ka ajiye gidanka, har take rashin lafiya, saboda iskanci a gabana kuma kake waya da ita?" Ya girgiza kai ya ce "A'a ba karuwa ba ce Daddy..ammm.... "Abdul, yanzu ba zaka daina sakarcin nan ba, sai abokan adawa sun farga, sun fitowa da duniya waye kai? Uban wa zai yadda ya zaɓeka, idan mutane suka san you are womanizer? Kuma har ka ajiye mace a gida, bama ka yi shahshashancin ta tafi ba. Na haramta maka kwana a waje, duk in da kake ka dawo gida ka kwana, kuma a cikin watan nan za ayi bikinka, ko ka yarda ko baka yadda ba". Abdul ya kalli Indabo ya ce "Dan Allah Daddy ka bari na kawo wadda nake so na aura, ni wallahi bana son waccan yarinyar, ni ka bari zan yi maka bayani" "Babu wani bayani da zan saurara daga gareka, dan nawa bayanin ne gaba da naka, kuma kaje ko sallami koma wace karuwar ce daga gidanka, tun kan na biyoka na ci maka mutunci" cikin sauri ya fice, yana sake kiran rahama, a ransa yake jin sai dai ayi wadda za ayi, ko da kuwa hakan yana nufin bayyanawa duniya ramma ne. *** Yana tsaye a jikin bishiya, ya juya wa hanyar da take tahowa baya, yayi crossing ƙafarsa, hannunsa ɗaya riƙe da taba, ɗaya kuma yana danna wayarsa. Daga bayansa kawai, sai mutum ya so ya juyo ya ga fuskar sa, suffarsa ta ƙaƙƙarfan namiji duk a bayyane, saboda yadda damtsensa yake a murɗe, ya cika hannun shirt ɗin sa, hannunsa ɗaya kuma ya sha ɗinki. Rigar ja sai dogon wandonsa baƙi. "You are under arrest, officer ku kama shi" ko motsi bai yi ba, balle ya waiwayo, ta zagaya ta gefen bishiyar, tana leƙa fuskarsa, ya ɗaga kai ya kalleta ta ce "Kai baka jin tsoro ne?, ba ka ji tsoro ba da na ce you are under arrest" ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Tsoro?" Ta ce "Eh mana" "Hmm" kawai ya ce, ya zuƙi sigarinsa, ya kawar da kansa gefe, ya din ga sakin hayaƙin, in a passionate way" Ta zuba masa ido, komai nasa na daban ne, kuma na musamman. "Wurinka na zo" Ya ɗaga mata idonsa da girarsa ɗaya alamar yana jinta, hakan ya sanya ta ɗan diririce. Ya samu wuri ya zauna, ita ma ta zauna, ta kalleshi ta ce "Sannu ya hannunka? Na ga da sauƙi ma baka da ƙan jiki" ya kalli ciwon, ya basar, ya sake zuƙar sigarinsa. Yana sakin hayaƙin, ta fara tari, ya kashe sigarin a jikin bishiyar, ya ce "Ina jinki". Tayi gyaran murya ta ce "Raina ma fa babu daɗi, shari'ar nan da nake yi, so suke su yi mink fin ƙarfi, na fara sarewa kuma hope ɗin iyalin mutumin duk a kaina yake, ni da na gansu ma sai in ji zan yi kuka" tayi maganar tana goge hawayenta. "Ohh, a haka za a tsaya mini? Idan bamu yi nasara ba, sai mu zauna mu yi kuka?" Ta girgiza kai ta ce "A'a zamu yi nasara in sha Allah, shaidar fa da na gabatar babbar shaida ce, wani ya turo mini voice na maman Yarinyar, tana kuka ta ce a taimaka mata, amma wanda ya turo ɗin yayi blocking ɗina, sai kuma aka ajiye mini wannan a office ɗin" tayi maganar tana ciro file ɗin tarihin Naja bunkure ta miƙa masa daga cikin jakarta ta goyo. Ya karɓi file ɗin ya fara dubawa, ya miƙa mata hannunsa, ya ce "Bani wayarki" ta ce "Wayata?" Yayi shiru yana kallont, dan ba zai maimaita ba. Ta ciro ta cire password ta miƙa masa, ya karɓa yana dannawa. Ta zura kai tana leƙa wayar, ta ce "Me kake nema a wayar?" Ya janye wayar ya cigaba da dannawa. Kiran Nasir ne ya shigo, ya miƙe mata dan ta ɗaga, ta girgiza masa kai ta ce "Rabu da shi" "Ki ɗaga ki gaya masa muna tare, ba nemana yake yi ba?" Ta kalleshi ta ce "Ga wayar nan a hannunka, ka ɗaga ka gaya masa" kafin ta rufe bakinta, ya yi accepting call ɗin, ya kai wayar kunnensa. Ayshercool 08081012143 56 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Wata irin zabura Nabila tayi, ta kai hannunta zata karɓe wayar, amma ya riƙe hannunta yana kallonta, girgiza masa kai tayi da sigar magiya tana kallonsa. "Hello. Hello, Arfa" muryar Nasir ta fito rangaɗau a wayar. Viper ya ɗaga idonsa yana kallon ƙwayar idonta, ga mugun riƙon da ya yi wa hannunta da take jin tamkar zai ɓalle. "Arfa kina ina ne? Hello kina ji na?" Kallon da Viper yake yi mata, gaba ɗaya sai ta rikice, ga kusancin da suke da shi, ta ƙara rikicewa. Kasa daurewa tayi ta ce "Wayyo hannuna" "Nabila, menene? Kina ina ne?" Al'amin ya sakar mata hannunta, ya katse kiran, ta ja da baya tana murza hannunta tana ƙifta ido. "Amm meye ma sunan naki?" Ta kalleshi tana turɓuna fuska ta ce " 'yar madara" Cikin sauri ya kalleta ya ce "Iyee?" "To idan ban kai 'yar madara ba, ka din ga ce mini 'yar suga, ko mazarƙwaila" tayi maganar tana cigaba da murza hannunta. "Baki shiryawa wannan ranar ba, ki ka yi gammon ɗaukar abun da baki san a ina zaki sauke ba?" Ta gyara zamanta ta ce "Nayi mana, ai shi ramin ƙarya ƙurarre ne. Amma yau  da ka gaya wa DSP muna tare, da ka gama kashe ni da raina, ban gama da aikin gabana ba, ka sake ɓallo mini ruwa. Zaman kotun nan na yau ya bani haushi, Alƙalin alamu sun nuna side zai ɗauka, gashi dattijon nan ya musa ya ce ba shi bane ba, sun kafa hujja da shi ne, wai lokacin da abun ya faru daga shi sai ita, kuma ita da shi da wata mai aiki ne, amma har gidan ɗayar  naje ban same ta ba. Su kawo ita rammar kotu, ba su kawota ba, ba su da wata tabbatacciyar shaida, recording ɗin da na gabatar, an soke an ce sai dai uwar taje da kanta, ni na rasa me ma zan yi wallahi" tayi maganar cikin matsananciyar damuwa. Ya nuna mata file ɗin hannunsa ya ce "Waye ya baki wannan?" "Ban san waye ba, a kan teburina kawai na ganshi da safe" ya cigaba da daddana wayarta, ba tare da ya kalleta ba ya ce "Kin ɗauki hotona, dan ki nuna wa yayanki ya kama ni?" Ta kalli wayar hannunsa, ta ce "Ai nayi hiding ɗin hoton, ya aka yi ka buɗe?" Ya sake kallonta ya ce "Me kike da hotona?" Nabila ta ce "Saboda in din ga kallonka, ina jin daɗi, askin nan da aka yi maka kayi mini kyau sosai da sosai ne" tayi maganar tana murmushi. "Amm, amma dan Allah ina ka tafi, naji su Oga walid sun ce, ɓata kayi, wai ranar da muka rabu ina ka tafi? Can ka koma ko? A can aka ji maka ciwon nan. Na tsorata da naga an yanki cinyar wani, da sun ganni nima kasheni za su yi ko?" Gyaɗa kai yayi, ya ce "Kina da system?" "Eh tana gida amma" ya cigaba da danna wayarta. "Wai dama kana magana haka? Baka taɓa yi mini doguwar magana ba sai yau. Hmmm da tabon wuƙarka da ka yi mini zan koma ga Allah, ka kusa fa kashe ni ranar farko da muka haɗu, ban san laifin da nayi maka ba ka kusa kashe ni. Amma dai yau ba ka sha komai ba ko? Naga yau ka yi mini kirki" jefa mata wayarta yayi ya tashi tsaye, ya ce "Ki kula da kanki, ana bibiyar ki, ana bibiyar wayar da ki ke yi da wata sumayya, akwai alamar tana bin diddigin abubuwan da ki ke yi, ko kuma ana bibiya bata sani ba". Ta tashi tana zare ido ta ce "Sumayyan?" "Wanda yake bibiyarki, shi ya turo miki wannan voice ɗin, ya baki tarihin bunkure, duk da bai baki complete ba. Yana bibiyar ki ko dan ya taimake ki, ko kuma yana da manufar da yake son cimma, dan haka ki kula" Ta dafe ƙirji ta ce "Amma meyasa za a din ga bibiyata da sumayya? To wa ka ke tunanin yana bibiyata? Ka yi mini bayani sosai da sosai to me ma nayi za a bibiye ni?. Ya cigaba da tafiya bai bata amsa ba, tabi bayansa tana cigaba da magana. Ya tsaya cak, ya waiwayo ya kalleta, tsayawa tayi ita ma, tana kallonsa tana jiran taji mai zai ce?. "Kin haɗu da Indabo?" Shiru ta yi, sai kuma ta waro ido ta ja da baya, ta ce "Wai indabo ɗan siyasar nan, shi ne dai na cikin labarinka? Na ganshi a wurin aikin su sumayya, subhanallah shiyasa tun a ganin farko da nayi masa naji na tsane shi". "Ya ganki?" "Eh, sai dai ban kula shi ba. Ai ni bai sanni ba, nima kuma ranar na fara ganinsa, sunansa kawai nake ji, amma menene?" Ya girgiza kai ya ce "Shikenan" ya cigaba da tafiya. Ta sake bin sa tana ɗan haɗawa da gudu, saboda saurinsa ya fi nata sosai, "To ka yi mini bayani, ni menene haɗina da shi to?" "Babu, ki je ki mayar da hankali a kan wannan case ɗin, idan kin yi wining sai ki dawo, kar na sake ganinki a wurin nan" Cikin rashin fahimta ta ce "To amma" "Take your way, ki tafi na ce" yayi maganar yana nuna mata hanya, ƙyam ta tsaya tana kallonsa, mamaki ne ya cika shi, tsawar da yayi mata ko a jikinta, ta tsare shi da idanunta masu matuƙar haske, yanayin yadda take abubuwan ta, ya sake tabattar masa da akwai sangarta a tare da Nabila. Ya juya ya tafi, ita kuma ta tsaya cak, tabi bayansa da kallo, tafiyarsa kawai gwanin burgewa, tafiya yake yi cike da ƙasaita, da bayyanar da ƙarfin da yake da shi, sai dai shi bai san yana hakan ba, har ya ƙulewa ganinta, sannan ta juya ta fara tafiya. Sai yanzu take wasu lissafe-lissafe, tabbas sumayya ta canza, sun rage yin waya sosai yanzu, kuma ba ta kiranta da layinta sosai yanzu, kenan da gaske haɗa baki aka yi Sumayya a bibiyeta? To waye yake bibiyar ta ta? Farar motar nan ce ya faɗo mata a rai. "To idan kuma an san ina zuwa nan fa, aka tona mini asiri, ina zuwa wurin mai laifi da ake nema ruwa a jallo. Wace amsar zan bayar na kare kaina?. "Wai me ma ya aike ni tun farko? Ina zaman zamana" tana tafe a hanya, wani irin ciwon kai ya saukar mata, da kyar ta ƙarasa gida. *** A kwance Abdul ya tarar da ramma, cikin damuwa ya ce "Rahama ya aka yi baki da lafiya, har na fita baki gaya mini ba?" Ta yamutsa fuska ta ce "Na zata zan warke ne, ba sai na sha magani ba" "Wannan ai ganganci ne, ko dai ciki ne?" Da sauri ta ce "A'uzibillah, Allah ya yi mini tsari, ai kai ma ka san ba shi bane ba" "Duk da haka, sai na gwada" first aid drower ɗin sa ya buɗe, yayi mata gwaje-gwaje, babu ciki sai malaria. "Rahama, wurin nan babu sauro a ina ki ka samo malaria kuma?" Ta kalleshi ta ce "A jikinka" Yayi murmushi, ya haɗa allurai, zai saka mata cannula, ta hau kuka wai ba ta so. "Rahama kina wahalar da ni, yanzu alluran baki zan yi ki shanye ko kuwa?" "Ni hannunka da zafi gaskiya, ka samo wani yayi mini" ya harareta ya ce "Wani wa? Babu wani mahaluki da zai ganar mini jikinki a doron duniyar nan, ina kallon shi" "Eh amma ai kai ka iya kallon na wasu" "Duk cikin aiki ne, kuma ki yi mini shiru nayi aikina, ko na caccaka miki allurar har a baki" Ya saka mata cannula, yayi mata allurai, ya saka mata ruwa, da duk ya ajiye su a gidan, saboda ramma. Ya rungumeta a jikinsa, yana shafa saman cannulan, ɗaya hannun kuma yana matsa jikinta a hankali. Ya zubawa hannunta ido, daga lokacin da ya ɗaukkota zuwa yanzu, ta canza sosai da sosai, fatarta tayi kyau, tayi haske. Ramma ba wani shahararren kyau ne da ita ba, amma yana jinta a kusa da zuciyar sa, duk da ba wani shiri suke yi ba, duk in da ya tafi tana ransa. Bai taɓa raping ɗin mace ba, sai a kan ramma, hakazalika bai taɓa tarayya da virgin ba sai ita. Bai taɓa jin kunya da dana sanin wani rashin mutunci da ya yi ba, sai a kan abun da yayi musu, yanzu kuma uwa uba, ɓatan mahaifiyarta, bai san me zai ce mata ba, duk da yana ta ƙoƙarin ganin ya gano in da take. Yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Sannu, kan ya daina ciwo?" "A'a, amma Alhamdilillah ya rage" "Masha Allah, ki bani labarin ƙauyenku mana, zan cika alƙawari, na yi magana da ɗan majalisar ku, lokacin da naje Abuja, zai shigar da ƙudurin hanyar ku, burtsatse ma da ki ka ce, ina jiran injiniyoyi su gama lissafi su turo mini, za ayi muku guda uku" ta tashi zaune ta kalleshi ta ce "Da gaske dan Allah?" Ya jinjina mata kai yana murmushi, itama murmushin ta yi, ta ce "Yan garinmu za su ji daɗi, mun gode Allah ya saka da alkhairi, mun gode sosai, yan garinmu mun daɗe muna koken rashin hanyar nan, amma ba ayi mana ba, mun gode" "Yau ba Allah ya isan?" "Ai wancan abun da ka yi mini daban, wannan ma daban, amma Allah ya isa tana nan" Abdul ya yi ajiyar zuciya ya ce "Ki yafe mini mana sweetheart " Ramma ta ce "Ka mayar da ni wurin mahaifiyata, ka nemi afuwarta, amma haryanzu a zuciyata ban ji zan iya yafe maka ba, daga kai har anty maijidda, da wannan bayahudiyar matar" Yayi shiru ya sunkuyar da kai, zuciyarsa babu daɗi, ta ɗaga kai ta kalli fuskar sa, ta ce "Oho, ba zaka bani tausayi ba, ka tuba ga Allah ka gyara halayenka, dan ka samu kyakkyawar makoma. Ka cigaba hannun ya fara zafi" bai ce mata uffan ba, ya cigaba da shafa mata hannun. Ta saka ɗaya hannun ta juyo da fuskarsa, taga idanunsa sun yi ja, sun bayyanar da tsantsar damuwa. "To meye kuma?" Ya girgiza kai alamar babu komai. "Ka tabattar?" Ya jinjina mata kai alamar eh. "Shikenan, to kayi haƙuri dai, ni gaskiyata na gaya maka, baka san zafin abun da ka yi mini bane, amma naga kamar ka ji haushi" "Meyasa zan ji haushi, carbi zan sayo ki zauna ki yi ta jan Allah ya isan son ranki" ta murguɗa masa baki, ta kawar da kanta gefe. *** Madaki ya zuba wa cinyarsa ido, yadda ciwon da Viper ya ji masa yayi wani irin mugun rami, maimakon ya yi ja ma, sai ya koma yayi kore, wasu irin jijiyoyi duk suka ɗaɗɗaga a gefen ciwon, ƙafar ta ƙara riƙewa, ba ya iya takata sai dai ya dinga jirgata. Ya kalli babban amintaccen yaronsa ya ce "Lakwari, ciwon nan fa cigaba yake yi, kenan ta tabatta alkadarina ya karye?" "Nima na gani maigida, kaga ana ta saka maganin, amma sai cigaba yake yi. Ba zamu yi saurin yanke hukunci ba, mu bi dare kawai, muyi makabeli mu ɓace mu yanka gabas, mu koma in da aka fara, ya duba mana, idan da wani abu da za a yi a kai, idan ba haka ba, mai zamani ya yi maka muguwar illa, kuma yana sane yayi hakan". Madaki ya jinjina kai ya ce "Haka ne, babban abun da ya bani mamaki, bai wuce wanda suka zo suka ɗauke shi ba, ban san suwaye ba. Ta tabbata yana da waɗanda suke goge laifukan da yake aikatawa, yakamata na sanar da indabo" Lakwari ya ce "Haka ne, amma mu fara neman mafita, a karya dafin nan da ya saka maka, kafin duk wata magana ta biyo baya". Ya jinjina kai ya ce "Shikenan". *** Sumayya da murtala ne a zaune a gaban MD sun yi fiƙi-fiƙi da idanu, gefe ga lawisa a zaune. "Abun da ku ke yi, da kai da sumayya ya fara yawa a wurin nan, ko dai ku bi tsarikanmu, da abun da muka ce dan cigaban tashar nan, ko kuma ku ajiye mana aikinmu. Duk jajircewarku akwai waɗanda suka fiku. Gashi kun saka hankalin mutane gaba ɗaya ya yo kanmu, saboda recording ɗin da ku ka saki a duniya da yake bayyanar da zargi ga Naja'atu Bunkure, wands duniya kowa ya shida mutuniyar kirki ce, mai yi wa mutane hidima". Murtala ya ce "Tuba muke, muna neman afuwa in sha Allah ba zamu sake ba" "Daga kai har ita, wannan ne karo na biyu da kuka aikata mana laifuka, muna ƙyaleku, na uku kora ce. Yanzu dole mu san yadda zamu yi mu gyara wannan shirmen da kuka yi" Murtala yayi ta bayar da haƙuri, sumayya kuwa fafur ta yi shiru, taƙi cewa komai. Sun fito daga ofishin MD, tana hura hanci, ta tarar da Nabila. Sumayya ta ƙarasa ta zauna a kusa da ita, ta ce "Ke kuma daga ina? Kin je kin haɗa kai da Uncle murtala, mun saka recording ɗin da yayi miki, a kan shari'ar nan, yanzu aka gama sauke mana kwandon jaraba a ka. Nabila ta ƙurawa sumayya ido, ta ce "Sumy why?" Cikin rashin fahimta ta ce "Kamar yaya?" Nabila ta yi murmushi ta ce "Don't mind me, mota fa ta iso, na zo na sanar miki" Ihun farinciki sumayya tayi ta ce "Are you serious, ko kuma jirgani ki ke yi?" "Da gaske nake, amma Abba ya ce ba zan hau ba, sai driving licence ɗina ya zama ready, kin san shi da ƙa'ida" Cikin farinciki ta ce "Alhamdilillah, summa Alhamdilillah yawo ba kama ƙafar yaro, Allah ya saka wa Abba da alkhairi, uban marayu mai uban ma goyawa yake yi. Amma dan Allah arfat ki kula, ki san in da zaki din ga zuwa, banda rigima da faɗa da mutane a titi" ta din ga kallon sumayya, da son tabattar da abun da Viper ya gaya mata, yanzu sai ayi amfani da ita, a cutar da ita, sam ta kasa yarda gaba ɗaya. Wada M karofi ne ya kira Nabila a waya, ta ɗaga ta ce "Hello sir" "My beautiful angel, ya kike yau bamu gaisa ba gaba ɗaya, kin ƙi bari mu haɗu, gashi na koma wurin aiki" Ta ɗan kashe murya ta ce "Ba haka bane ranka ya daɗe, ka san aikin namu ne babu zama, amma very soon zaka zo har gida mu gaisa" yayi murmushi ya ce "To shikenan, na san maybe kina wurin aiki, da daddare zamu yi waya in sha Allah" "Ok Allah ya kaimu, ka kula da kanka sosai, kar ka yi aiki ka gaji da yawa" Yayi dariya ya ce "Thank you my dear" Sumayya ta ce "Ohh wa kuma ake yaudara, wa aka kwaso mana?" Nabila ta bata labarin wada M karofi. Sumayya ta ce "Allah ya sa shi ne mijin, kakarmu ta yanke saƙa, kin san waye mutumin nan kuwa Arfa? Allah ya tsaga miki farinjinin manyan mutane, kar ki yi mana buƙulu dan Allah". Nabila ta tashi ta ce "Taɓ gaskiya ba na son shi, ki zo gida kiga motarmu" Sumayya ta ce "Dolena" Nabila tayi mata sallama ta fito, zuciyarta na cigaba da wasi-wasi a kan Sumayya, har ga Allah tana ƙaunar sumayya har cikin zuciyarta, ta kasa yadda da abun da Viper ya gaya mata. Nabila na tafiya aka kira Sumayya a waya, ta ɗaga tayi shiru. "Sumayya meyasa ki ke wasa da rayuwar ki, da ta ƙawar taki ne? Bayan ɗan waken zagaye da ki ke yi, Ki ke kiranta da wasu layukan daban, shi ne ki ka yi disconnecting ɗin bibiyar kiranki da ita da muke yi ko?" "Ni kuma, ban gane nayi disconnecting ba? Wallahi ban yi disconnecting ba" "Ƙarya ki ke yi, some hours back, aka yi disconnecting, zaki ga matakin da zamu ɗauka a kanki da ita, sannan zuwan da tayi me kuka tattauna?" Sumayya ta dafe kanta ta zauna, sannan ta ce "Mota aka saya mata, sai labarin sabon saurayinta da tayi, Alhaji Wada M karofi, sai ƙorafin rashin nasara da take hangowa a kan shari'ar da suke yi". P.A ya maimaita "Ki ka ce Alhaji wada M karofi?" "Eh, shi" "Ki cigaba da sanya ido a kanta, kina kawo mana rahoto, akasin haka zaki ga abun da ba kya so " ta kashe wayar ta dafe kanta. *** "Indabo ya ga yarinyar nan" Gaba ɗaya suka kalli Al'amin, liti ya ce "Shikenan, ai na san a rina" Walid ya ce "Ya aka yi ka gane haka?" "Mun yi magana da ita sosai yau, ana bibiyar ta, ana bibiyar kiranta da wata ƙawarta, na yi disconnecting duk wata hanya da za a cigaba da bibiyar kiranta. Amma rayuwarta na cikin hatsari, kuma idan ta cigaba da zuwa za a gane inda muke". Liti ya ce "Shiyasa tuntuni na ce, a sallameta ta daina zuwar mana nan, amma walid ya nace". "I think i will sealed a deal with her" Suka haɗa baki suka ce "Kamar yaya?" Yayi shiru yana lissafa yatsun hannunsa. Liti ya ce "Ka yarda da ita ne? Ni haryanzu tantama nake yi a kanta ne" Walid ya jinjina kai ya ce "Lallai a tafawa mata" Viper bai sake ce musu komai ba daga haka, ya tashi ya fita. *** M karofi yana zaune yana shan shayi, wani jami'in tsaro, ya shigo da Indabo cikin falon. Karofi ya kalli Jami'in tsaron ya ce "Zaka iya tafiya" ya mayar da idonsa kan Indabo ya ce "Barka da zuwa sirikina, kwana da yawa, muna haɗuwa a Abuja, amma da ni da kai, babu wanda yake ziyarar wani. Duk ni yakamata ace ina kawo gaisuwa. Bisimillah zauna mana. Indabo ya zauna, ya kalli M karofi ya ce "M karofi" "Ma'aruf Indabo" "Sabo da kaza fa, baya taɓa hana a yanka ta" Karofi ya ce "Wannan haka yake, ko a siyasance, ko ma a normal life" "Auren 'yar uwata maijidda da kake yi, ba zai hana idan kayi mini kan kara nayi maka na itace ba, hawainiyarka ta kiyayi ramata" Yayi murmushi ya ce "Yakamata kayi mini fashin baƙi, akan wannan kurman baƙin da kake ta karanta mini" Indabo ya yi wata ƙwafa ya ce "Soyayya da ka je ka fara da 'yar cikinka, saboda abun kunya, kuma yarinyar da take ta gwagwarmayar sai ta tona mana asiri, wadda ka tsayawa, wallahi muddin asirin Abdul ya tonu kaine ba wani ba, kuma sai nayi maganinka a siyasance da duniyance" M karofi ya ce "Iko sai Allah, kana nufin Nabila wai? Taɓ ai ni ban taɓa sani ba, banda yanzu da kake gaya mini. Ina da lawyer a law firm ɗin su, shi naje gani, na ganta naji ina sonta, kai idan nayi niyyar tonawa ɗanka asiri, da wani zancen ake yi ba wannan ba. Kuma ni ban yi abun kunya ba, sonta nake yi da aure. Tun da ƙanwarka ba yar gwal bace, da zata hanani zama da mata ba. Naji daɗin wannan gargaɗi da kayi mini sosai da sosai, amma ka kwantar da hankalinka, babu ruwana da shari'arku, nima aikina nake yi. Zaka iya tafiya idan baka da abun cewa". Indabo ya tashi, ya kalli idon kankarofi ya ce "Kifi yana ganinka mai jar koma" Karofi ya ce "A juri zuwa rafi dai " Indabo ya fice yana baza babbar riga. *** Nabila ta sake komawa gidan abokiyar aikin ramma, amma still bata same ta ba, aka sake gaya mata ta koma garinsu, sai dai samun sunan garin ma ya gagareta, ta kasa samu. Tana kwance a kan gadonta, ta buɗe videos da hotunan da ta yi wa Viper, ta zuba masa ido, tana jin daɗin tsokanarsa da take yi, na cewa tana son shi, tana son zama kishiyar 'yar madara, mugun kallon da yake yi mata, ba ƙaramin dariya yake bata ba. Mussaman da ta samu ya kulata, a haɗuwar su ta ƙarshe, duk da a ƙarshe, korarta yayi. Tana kallon hotunan tana murmushi, ta ɗauki ƙaramar wayarta, ta saka lambarsa ta kira. Sai da ta kira da ainihin lambarta, sannan ya ɗaga. "Ohh Allah, kayi saving lambata ne?, Ina ta kiranka da ɗaya layin amma baka ɗaga ba. Ina ta kallon hotunanka, ina son in yi bacci . Ka san ranar da nayi maka hotunan nan, har murmushi fa kayi, ka din ga fara'a murmushi yana yi maka kyau sosai dear. Yaushe zaka ƙarasa bani labarinka ne? Yakamata ka gabatarwa jauhar ni, a matsayin amarya, zan yi mata biyayya sosai da sosai, in tayata sonka. Ba zan yi kishi da ita ba, ina sonta sosai da sosai, dan Allah ko sau ɗaya ka haɗani da ita mana" kamar da iska take, haka yayi shiru ya ƙi magana. Ba ta gaji ba, ta sake cewa "Ina ƙaunar yar madara saboda Allah, dan Allah ka ƙarasa mini labarin ta". "Meyasa ki ka shigo rayuwata?" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Labarin dogo ne, ba zan ɓoye maka ba, da dai ina taya Yayana nemanka ne, saboda nayi suna, na rama abun da Bunkure ta yi mini, na wulaƙanta ni a gaban jama'a. Shi ne na din ga up and down, har na haɗu da wannan litin, mara kirki". "Saboda ki yi suna ki ke son taimakona?" Nabila ta ce "Eh, a da ba, amma jin labarinka gaba ɗaya ya canza mini tunani, nake jin zan iya yin komai, dan na ga na ƙwato maka hakkinka, da kai da yar madara, duk da ban san ƙarashen labarin ba. Amma gwiwata ta fara sanyi, na fuskanci Naja'atu Bunkure nan, tana da goyon baya daga sama, kuma indabo babban mutum ne shahararre sosai, ina buƙatar support sosai, kai kuma sai korata kake yi kana hantarata". "Idan na ƙarasa miki labarin, that means duk tsanani babu gudu babu ja da baya, zaki tsaya a shari'ata komai wahala da sarƙaƙiyarta?" "In sha Allah, i promise it" Ya sake cewa "Kin tabattar zuciyarki zata iya ɗauka komai muni, komai daɗin abun da zaki ji?" Cikin ƙwarin gwiwa ta sake cewa "Eh zan iya" Viper ya ce "Take your time to think, ki yi comparing da ƙalubalen da ka iya biyo bayan hakan" Ta lumshe idonta, hatta muryarsa, mai daɗi ce, duk a buɗe take saboda bayan naturally yadda take, wiwi da shaye-shaye sun ƙara making ɗin ta deep. Ba ta bashi amsa ba, ya kashe wayar. Walid ya ce "Mai zamani, ka yadda da maganarta kenan? Zaka ɗauki fansa ta hanyar shari'a" Mai zamani ya girgiza kai ya ce "Ta riga ta shiga tarkonsu, kuma na fuskanci ba ta ji ko kaɗan, zata iya salwantar da rayuwarta". Walid ya yi murmushi mai cike da jin daɗi ya ce "To ɗaya maganar fa? Zaka gaya mata?" Al'amin ya kalli walid, yayi shiru bai ce komai ba. *** Jikin ramma da sauƙi sosai, tana zaune a gefen gado, Abdul yana bata abinci, gefe ga magungunan ta. Wayarsa da take ringing ya ɗaga ya saka a hansfree ya ajiye  ya ce " 'yar mutanen bunkure, ya ake ciki ne?" "Abdul" "Na'am" "Ya ka yi da yarinyar nan ne da ka yi wa fyaɗe? Wata yarinya ta tsaya kai da fata, sai ta wanke dattijon nan, mun yi duk abun da yakamata, ta koma tana amfani da social media against me, hankali na ƙoƙarin dawowa kaina, sai sintiri take yi wai lallai sai an kai yarinyar gaban shari'a, ga wani voice message da yake yawo na uwar yarinyar...... Abdul ya cire wayar daga hansfree, ya saka a kunnensa, yana kallon ramma. "Ka gaya mini yaya ka yi da ita? Tana raye ko ta mutu? Mu san abun da zamu shirya a kan shari'ar, an je gidansu babarta bata nan an nemeta an rasa" "Kina ji? Zan zo in anjima yanzu ina wani uzurin ne" ya kashe wayar, ya kalli Ramma zai yi magana, amma ya kasa saboda mugun kallon da tayi masa. "Rahama ki tsaya ki saurare ni ki ji" "Kayi mini shiru tun ba shaƙeka ka mutu na huta ba, azzalumin banza da na wofi, in sha Allah sai Allah ya tarwatsa ka da kak kai da duk masu goya maka baya kuna cutar mutane" Fafur ta ƙi saurarsa, tayi watsi da kayan karin kumallon, ta tashi ta bar masa ɗakin. *** Nabila ta daina shiga harkar Nasir, dan sosai ya sakata a gaba, da masifar lallai sai ta daina case ɗin bunkure, saboda lafiyar ta da rayuwarta, ita kuma ta ce babu wanda ya isa. Sumayya ce ta kirata da wata lamba, ta ɗaga ta ce "Waye?". "Ke ni ce" Nabila ta ce "Yar 419, yau kuma da lambar wa ki ka kirani, ko aiki ki ke yi a kaina ne?" "Nabila, bar wannan maganar kin san menene?" "No" "Maganarki da muka saka a radio, a kan bunkure, wata mata ta zo mini, ta ce lallai ke take son gani, akwai information da zata baki a kan bunkure, ta ce macuciya ce, abun babu daɗin ji, bama itakaɗai ba, akwai gwarama, mutane sun fara magantuwa fa" Nabila ta ce "Abubuwa sun fara yi wa kaina yawa, zan zo har gida na same ki" Ta ajiye wayar ta dafe kai tana tura baki. Duk da tayi farinciki da haka, dan kuwa gagarumin cigaba ne, amma gaba ɗaya ba ta yadda da sumayya ba yanzu, dole tana buƙatar ganin Viper kafin tayi wani yinƙuri. Babu tsammani ta ga Nasir ya shigo office ɗin ta, ta tashi tsaye ta ce "Yaya lafiya?" "Nabila wai ke meyasa a duniya ba kya nemawa kanki zaman lafiya ne? Gaba ɗaya na kasa gane kanki a 'yan kwanakin nan, menene yake damunki ne?" Cikin rashin fahimta ta ce "Me kuma nayi?" "Comment ɗin da ki ka yi da safe nake magana a kai" yayi maganar yana ciro wayarsa ya daddana, ya buɗe facebook ɗin sa, ya tura mata wayar. Ta kalli wayar, posting ne da hukumar yan sanda tayi, na cigaba da neman Aminu Viper ruwa a jallo, saboda ayyukan ɓarna da yake cigaba da yi. Tayi comment da "Wannan abun kunya ne ga rundunar tsaron Nigeriya, ace kuna tsare da mutum a prison, a sake shi kuma a dawo ana nemansa, ba shi ne abun bincike ba, hukumar 'yan sanda, da prison, da ta shari'a su ne abun tuhuma da zargi" aikuwa mutane suka yi caa a kan comment ɗin ta, suna reply. "Yanzu yaya fisabilillahi menene laifina a cikin wannan comment ɗin nawa, ita hukumar 'yan sandan, dan ayi comment ai suka yi posting ɗin, kuma gaskiya na faɗa. Akwai ayar tambaya a kan ma'aikatar Shari'a, hukumar yan sanda da ta gidan yari a kan case ɗin nan, kar ka yi wani tunani daban, ina goyon bayan gaskiya ne kawai" "Nabila ba kowane lokaci gaskiya take tasiri a ƙasar nan ba, yanzu ki ka shigo cikin system ɗin nan, ƙasar nan ta wuce duk yadda kike tunani". "Na sani, amma rashin yin wani yunƙuri na kawo gyara, shi ne ke kawo mana koma baya yaya, ba wai ina goyon bayan Aminu Viper ba ne ba, menene gaskiyar abun da yake faruwa nake son sani" Cikin takaici ya girgiza kai ya ce "Idan kin ƙi ji, ba zaki ƙi gani ba arfa". Ya ɗauki wayarsa ya juya ya nufi hanyar fita, ya kama handle ɗin ƙofar office ɗin ya murɗa ya buɗe. Sai dai wanda suka yi ido huɗu da shi a tsaye ya sanya gabansa wani irin mummunar faɗuwa. Ya raɓa jikin Nasir ya shiga cikin office ɗin, Nabila ta waro ido tana kallonsa tana kallon Nasir. Ayshercool 08081012143 57 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Kallonta yake yi ta cikin baƙin glass ɗin idonsa, duk da ya saka facemask, babu yadda za ayi Nabila ta kasa gane shi. Nasir ya tsaya ya waiwayo, yana son sake ganin waye, duk da fuskarsa a rufe take da face mask, amma ya tsaya ƙyam a tsakiya, ya juya wa Nasira baya, yana fuskantar Nabila. A hankali ya ƙarasa takawa, yaje ya samu wuri ya zauna a kan kujera, ba tare da yayi magana ba. Nabila kuma ta kalleshi ta kalli Nasir. Nasir ya juya ya tafi, yana fita da saurin gaske ta ƙarasa, ta rufe ƙofar office ɗin ta saka mata key. Ta dawo ta kalleshi, ya cire facemask ɗin sa da glass ya ajiye a kan teburinta. "Su maciji an fito daga rami, kuma kai tsaye aka yo wurina,  dan Allah meyasa ka ke son lallai sai ka haɗu da yaya Nasir ne? Da ya gano ka da ni da kai zai haɗa duk ya kama, dan ban san me zan ce masa ba" Ta dafe ƙirjinta ta ce "Wayyo Allana, haryanzu zuciyata racing take yi, ranka ya daɗe irin haka sai ka kirani a waya, ka ce in zo kana son ganina, amma wannan dirar mikiyar da ka yi mini ohh my God me ma zan ce ne? Allah ya sa babu wanda ya sanka" ta zagaya ta buɗe fridge ɗin office ɗin ta, ta ɗauki plate ta ɗoro masa apple, ayaba da lemo ta zo ta ajiye masa. Ta tsiyayo ruwan zafi a dispenser ta haɗa masa tea mai zafi, ta buɗe jakarta ta ɗaukko ɗan ƙara min flask, ta juye masa dankali a kan plate da ƙwai, ta ce "Bisimillah, fara cin abincin sai mu yi magana naga yanzu safiya ce" yayi shiru yana danna wayarsa. "Ka ci abinci, wanne zaka fara ci?" Still bai yi magana ba, har ta fara jin haushi. "Sweetheart, magana nake fa, 'yar suga na magana" ya ɗago ya kalleta. Ta saka hannu ta karɓi wayarsa ta ajiye, ta ɗauki kofin shayin ta miƙa masa ta ce "Ba dan ni ba, dan Allah ka sha, a gabanka na haɗa, ban kuma son da zuwanka ba, balle ka ce na zuba wani abu a ciki dan Allah" tayi maganar cikin kwantar da murya. Ya saka hannu ya karɓa, sai dai kamar ƙaramin yaro, ya zubawa kofin ido. Ta ɗaukko plate ɗin dankalin, ta riƙe a hannunta, ta kalle shi ta ce "Sha mana" ya tsareta da idanunsa masu ban tsoro. Ta sauke nata idanun, saboda yadda nasa suka yi mata nauyi. Ta saka hannu ta kai kofin bakinsa, ya buɗe bakinsa a hankali, ya fara sha. Tayi ɓoyayyiyar ajiyar zuciya, ya sauke kofin, ta miƙa masa dankalin, kamar mai koyon cin abinci, haka yake ɗauka yana ci. "Yauwwa My dear" yana ci, Adam apple ɗin maƙogwaronsa, na kaiwa na komowa, sai yayi kamar zai yi magana, sai ya fasa ya haɗiye maganar tare da abincin, da ƙyar yake haɗiye abincin, a duk lokacin da ya saka abinci a gaba zai ci, haka yake ji, sai ya cakala ya bar shi, tun su liti suna lallaɓa shi ya ci abinci, har sun haƙura sun ƙyale shi, sun zuba masa ido. "Master, ciwonka ya gama warkewa, Alhamdilillah Allah ya ƙara tsarewa, ka daina zuwa in da za a cutar mana da kai dan Allah" Yayi mata shiru, yana cigaba da cin abinci. "Ko in ƙara gudun AC naga kana gumi" ya girgiza mata kai alamar a'a. Tana tayi masa hira, har ya cinye abincin tas. Ta ce "Alhamdilillah" ta miƙa masa tissue ya goge hannu. "Wai dan Allah meyasa kake ta kallona ne? Ko wani abun nayi?" Nan ma ya girgiza mata kai. "Kamar bacci ka ke ji fa, ko an sha ne?" "Me fa?" Yayi maganar yana kallon ta. Ta ce "Bakomai" "Aiki na zo yi" ya faɗa a taƙaice. Ta ce "Aikin me?" "Computer zaki bani" Ta ce "Ok, desktop ta aiki ce, bari na baka laptop ɗina" ta ɗaukki laptop ɗin ta ta bashi, ya buɗe ya fara dannawa. Ta zauna a kusa da shi, tana kallon mai zai yi, sai dai ta kasa gane me yake yi ɗin, wasu irin lambobi da alphabets kawai take gani a screen ɗin system ɗin. Sunan Yaya Nasir ne ya fito a kan wayarta, ta ɗaga ta kai kunnneta, tayi shiru. "Arfa" "Na'am" "Waye mutumin da ya zo office ɗin ki?" Ta kalli Viper sannan ta ce "Baƙona ne" "Wane irin baƙo?" Nabila ta ce "Client ɗina ne, ya zo muyi magana ne a kan wata shari'a meyafaru?" Nasir ya ce "Gaba ɗaya ban yadda da shi ba" "Daga fara ganin mutum yau ka ce baka yadda da shi ba yaya? Ka san shi ne?". "A'a kawai jikina ya bani wani abu ne, amma akan case ɗin menene?" "Is confidential, and against my professional ethics, ba zai yiwu na gaya maka ba, idan na dawo mayi magana" ta katse wayar. "Meyasa ki ke tsoron gaya masa ne? Shi ne DSP Nasir ɗin? Shi a yadda yaken nan matsoraci yake son kama ni, ai karo da karo sai rago, na raina jarumtarsa" Ta tsuke fuska ta ce "Ya haka? Yayana ne fa, banda cin fuska" Ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Da lokacin da nake mai zamanina ne, aka bashi aikin kama ni, sai na yi masa karayar da zai shafe shekara yana zaune yana jinya. A yanzun nan da muka haɗu, ba zamu rabu lafiya ba. Tarbiyyar Jauhar ce da girma ya sanya wasu abubuwan nake kawar musu da kai". Ta ce "A hakan? Yanzun ma fa kana zuwa ka sari mutane, ka yi faɗa da neman magana" Ya matso da fuskarsa saitin ta ta, ta ja da baya. "Lokacin da nake mai zamanina, bana bin ƙofa komai girmanta, sai dai na kama katanga kamar ɓarawo, bana biyo hanya ayi gaba da gaba da ni. Bana tsoron kowane irin nau'i na fitina ko tashin hankali, idan aka kwana biyu ban ji ni cikin rigima ba, sai na ji ni kamar mara lafiya. Aiki tuƙuru da jajircewa tayi a kaina, ba dan ƙaddara ta rusa tanadi da burikan rayuwata ba, ta ci kaso mafi yawa na tarbiyantar da rayuwata a kan tafarki madaidaici. Ki daina haɗa kanki da ita" Ta lumshe idonta ta buɗe ta ce "Shiyasa na ce tun da ita 'yar madara ce, ni kuma sai na zama 'yar suganka, amma ka ƙarasa mini labarin ta dan Allah" ya zauna sosai ya cigaba da danna system sannan ya ce "Idan na ƙarasa miki labarin ta, hakan na nufin we sealed a deal, da babu gudu babu ja da baya kenan, komai rintsi komai wahalarsa?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "A'a ki sake tunani, mussman ranar da zata fasu kina ɓoye shahararren ɗan ta'adda kamata" "Kai ba ɗan ta'adda bane ba, ta'addancin da aka yi wa rayuwarka, shari'a ta kasa tsaya maka ya sanya ka zama haka. A labarinka da oga walid ya bani, da tun a lokacin da aka kashe yayanka, hukuma tayi abun da ta dace, da duk ba a zo wannan gaɓar ba. Muna iya jure rashin makusantanmu ne, saboda ƙarfin imani, da tuna wanda ya bamu ne ya karɓi abunsa, amma idan wani ya zama sila, na rasa mutane masu muhimmanci a rayuwarmu, wannan imani na yarda da ƙaddara ya kan yi rawa a zukatanmu, mu kasa yadda da wanda ya bamu ne ya karɓa. Kai ba ɗan ta'adda bane ba mai babban suna, cin hanci a  doka da shari'a su ne suka mayar da kai duk abun da ka zama a yau. Ba kowace zuciya ce zata jure tana kallon wanda ya cutar da ita yana rayuwa cikin kwanciyar hankali, alhalin ita an bar mata tabo mara warkewa ta jure ba. Ban ce zan kai 'yar madara ba, amma na fuskanci giɓin da ka rasa nima akwai makamancin sa a rayuwata, da yake ci mini tuwo a ƙwarya yake damuna, ina ɓuya in yi kuka wasu lokutan na ji na tsani komai, kamar na kashe kaina na huta. Jin labarinka ya sanya, na fuskanci me ka ke ji a zuciyarka. Har abada duk tsanani ba zan sake kuskuren kallonka a matsayin ɗan ta'adda ba, kuma zan tabattar wa da duniya haka, da izinin Allah. Sai an gyara fannin shari'a an murƙushe rashawa da bambancin hukunci tsakanin ɗan talaka da mai kuɗi, mai ƙarami da babban uban gida, idan ana son rage yawan 'yan ta'adda" tun da ta fara magana, yake kallonta, duk da tana yi tana zubar da hawaye, hakan ya tabattar masa da akwai wani pain a zuciyarta ita ma. Ya juya ya cigaba da danna computer, ta kifa kanta tana goge hawaye. Ta kwantar da kanta a kan teburin, tana danna wayarta. Ta ɗaga idonta ta kalli, yadda yake ta sarrafa computer, bata san me yake yi ba. Yanzun ma hotonsa take ɗauka tana murmushi, kamar ba yanzu ta gama kuka ba. "Master" yayi mata shiru. Ta sake cewa "Maciji" tai maganar tana dariya. "Viper, maciji mai hatsarin gaske, yau ka fito daga raminka, ka zo wurina, sarana ka zo yi ne?" Still bai kulata ba. Ta tashi sosai ta ce "Da ni 'yar sugar da yar madara, wacce ta fi kyau ne? Kodayake na san ma ita zaka zaɓa, kafi sonta, amma dai kyakykyawa ce? Sannan fara ce ko baƙa? Doguwa ce ko gajeriya, ina son in ganta ka nuna mini hotonta, ko ba zaka bani haɗa ni da ita ba?". Sai da ya dafe goshinsa, Nabila bata gajiya da surutu, Jauhar akwai lokutan da ba ta kula shi da hira, idan ba ya cikin mood, shi wannan surutun nata ba zai bari su daidaita ba. Ya fizge wayar hannunta, yana dubawa yana danna computer. "Wai hacking ɗin wani zaka yi ne? Ni baka yi mini bayanin me ka ke yi ba, sonake ma mu yi magana, amma ka ƙi kulani, sai aiki kake yi kai kaɗai". Ya tashi tsaye ya ce "Zan yi salla" Ta nuna masa toilet, ya shiga yayi alwala, ya fito yayi sallar azahar, sanann ya kalleta ya ce "Tashi mu tafi" Ta tashi tsaye ta ce "Ina?" "In ƙarasa miki labarina, amma bisa sharaɗin da na gindaya miki da farko, babu gudu babu ja da baya, duk tsanani da wahala" ta jinjina masa kai. Ya ɗauki facemask ɗin sa ya saka, ya sanya baƙin glass ɗin sa ya yi gaba. Dama yau hijjabi mai niƙab ta sako, dan haka ta saka niƙabin, ta bishi. Cikin ikon Allah, chamber babu kowa, duk lawyoyin sun tafi kotuna, sai massenger da mai gadi. Suka fito, ta ce "To ina zamu je? Ba zai yiwu ka ƙarasa mini a nan ba?" "I have to test you more, before i completely trust you" daga haka ya tarar musu napep, ya gaya masa in da za su je. Suna tafe tana ta addu'a, Ubangiji Allah ya kare su, ya tsare duk in da za su je, Allah kar ya sanya ya cutar da ita, ko wani ya kama su. Kasancewar rana ce sosai, layin shiru babu kowa, suka tsaya a ƙofar wani gate, ya ciro mukulli a aljihunsa ya saka ya buɗe, ya ce ta shiga. Ta shiga sannan shi ma ya shiga ya rufe ƙofa. Ta tsaya tana kallon gidan, ya jingina da gate ɗin ya tafi tunani. "Waye yake mini kokowa da ƙofa zai karya mini gate?" "Ɓarawo ne ya zo sace matar gidan" tayi dariya ta ce "Da alama ɓarawon nan, bai san gidan wa ya zo ba ko? Ka bari mijina ya zo ya same ka" tayi maganar tana fitowa daga falon, fuskarta ɗauke da murmushi da tsohon cikinta. "Wai da ke muka haɗa kuɗi muka sai rigar nan ne? Ki din ga ɗaukar mini kaya kina sawa" Ta tura baki ta ce "Kai da kaya mallakar wuya ne, da kayan da mai kayan duk mallakin 'yar madara ne" tai maganar tana sakar masa murmushi. Nabila ta ce "Ya naga ka tsaya, ina ne nan?". Yayi firgita ya dawo daga tunanin da ya tafi. Ya tunkari ƙofar falon, zuciyarsa na bugawa da sauri da sauri, ya saka mukulli ya buɗe. Falo ne sosai, komai neat sai dai yayi ƙura sosai. Ta tsaya tana ƙarewa falon kallo, taji wani abu ya kama zuciyarta. "Viper, nan ne gidanka da 'yar madara tana ina? Kuma baka tsoron azo a kama mu?" Bai ce mata komai ba yama wuce ya shiga bedroom ɗin, ya tsaya yana ƙarewa ɗakin kallo, komai ya din ga dawo masa, tamkar mai mafarki. Tana tsaye, ya fito da wani riyo a hannunsa ya zo gabanta ya ajiye, yayi kneel down a gaban riyon, ya buɗe ya shiga fesawa kayan turaren florie. Ya din ga ɗago kayan, na jarirai ne, komai na haihuwa yana ciki intact, hatta zannuwa zamzam, bagaruwa, pad pampers komai akwai a ciki. Duk wanda ya ɗago sai ya fesa masa turaren ya ajiye, muryarsa na rawa ya ce "Ɗaya daga cikin ƙamshi mafi soyuwa a wurin jauhar kenan". Gaba ɗaya zuciyar Nabila ta tsinke, gabanta ya tsananta faɗuwa, ta ɗauki kayan, ita ma ta kai hancinta. "Yanzu tana ina? Ina kuma jaririn naga kayansa na jariranta haryanzu?" Ya ɗaga kai, yana kallon in da Nabila take zaune, ya ga jauhar kwance a wurin, cikin jini, tana ɗago masa hannun tana la'ila ha illa la, ya Allah. Daga nan bai sake sanin in da kansa yake ba, sai ji yayi an watsa masa ruwa mai tsananin zafi, da ratsa fata a jikinsa. Ya yinƙura zai tashi a gigice, amma yaji shi a ɗaɗɗaure, tamkar huhun goro. Ya buɗe idanunsa da ƙyar cikin matsananciyar galabaita, amma ya kasa magana, haka zalika wuyansa ya kasa tsayawa. "Idan ya watstsake, ku cigaba da tuhumarsa, har sai ya amsa laifin da bakinsa" "Ok sir" Suka cigaba da kwara masa ruwa mai zafi, amma sai dai ya zabura ya ƙanƙame jikinsa, amma babu baki. Suka kwance shi daga mugun ɗaurin da suka yi masa, sai dai ana gama kwance shi, ya faɗo ƙasa jikinsa a sake. Ɗaya daga cikin su ya ce "Haryanzu bai gama dawowa hayyacinsa ba, ku ƙyale shi tukuna" Indabo sai kaiwa yake yi, yana komowa a falonsa,ya rasa me ma yakamata yayi, gefensa ga P.A ga kuma madaki a zaune. "Wallahi kayi mini hauka madaki, ni ban san zaka yi mini sakarcin ba. Bambancinka da Aminu kenan, abun da aka saka shi yake yi, idan ka ga ya canza, to ya hango abun da ya fi naka ne, yanzu idan ya farka ya tona mana asiri ya kenan?" P.A ya ce "Honorable, ka kwantar da hankalinka C.P yana hanyar zuwa nan, zamu ji mai zai ce mana" Madaki ya ce "Honorable, da ka san hatsarin da yake tattare da yaron nan, da baka ce haka ba, mugun shu'umi ne. Hodar nan da guba na haɗata, kisa take yi har lahira, nayi mamaki da aka ce bai mutu ba, ba laifina bane ba, nayi iya ƙoƙarina". CP ne yayi sallama, ya shigo falon, suka amsa tare da mayar da hankalinsu kansa, ya miƙa wa Indabo hannu suka gaisa. Cikin zaƙuwa indabo ya ce "Yaya ake ciki C.P?" "Eh to, maganar gaskiya fa ya farfaɗo, kuma yana daf da watstsakewa a ko wane lokaci. Abun da muka yi guda ɗaya ne, a report ɗinmu, mun shigar da cewa ya sha kayan maye ne, ya bugu ya halakka matarsa". Indabo yayi shiru sannan ya ce "Kai naji daɗi, amma kamar hanyar ba tayi ba sosai, idan ya buɗe bakinsa, zai iya faɗar gaskiya fa" C.P ya ce ba zamu bari haka ta faru ba, lokacin da muka je gidan, mun goge duk wani abu da zai nuna hujjar wani ne ya shiga ya aikata laifin ba shi ba. Sannan mun ajiye miyagun ƙwayoyi har da hodar iblis, da sunan mun kama su a gidan. Idan za a fara sharia dole a samo ƙwararrun lauyoyi, kuma a yi wa alƙalin kyakykyawan gani, ni dai daga ɓangarena komai zai tafi dai-dai da yardar Allah. Tun da dama ya riga ya shahara kowa ya san ɗan daba ne" Indabo ya yi ajiyar zuciya ya ce "Haka ne, na gode sosai da sosai C.P, zaka ga saƙo da yardar Allah, kuma zan cika alkawarin da nayi, muddin komai ya tafi cikin nasara, amma C.P ba zai yiwu ku yi masa wani abu, ku kashe shi ba kawai?" Ya ce "No, muddin wani abu ya same shi, mu kuma zamu zama abun arziki, saboda sanarwar da kakinmu ya fitar mun tabattar da yana hannunmu cikin ƙoshin lafiya" "Shikenan babu laifi, na gode sosai da sosai" ya sallami C.P ya tafi, ya ce "Aikin Naja'atu ya zo, P.A kira wo mini ita". *** "Ka yi magana ka amsa laifinka, ka sauƙaƙa mana kai ma ka sauƙaƙawa kanka, idan ba haka ba mu zamu bi hanyoyin da zasu sama mana sauƙi" Al'amin ya ɗago da kyar, saboda a cikin mayen da yake, suka yi dukan tsiya, tamkar sun samu jaki, jikinsa ya ƙara mutuwa, kowace gaɓa ta jikinsa ban da ciwo, babu abun da take yi. "Ka amsa, ka ce ka sha kayan maye ka kashe matarka" Gefen bakinsa duk jini, sun tuɓe shi, daga shi sai vest da gajeren wando, ya sake ɗaga idonsa, karo na farko yayi magana ya ce "Ina jauhar?" "Ban sani ba, ni kake tambaya ina juahar? Bayan ka kasheta?" Tsaki yayi, ya taƙarƙare ya yinƙura ya tashi tsaye, suka saka kokara suka daki ƙafafuwansa, ya hantsila ya faɗi a wurin. Duk abun nan da ake yi, da jibgar da yake ci, shi kawai mafarki yake yi, jira yake yi ya farka, dan ba ya son baccinsa ya cigaba da nisa, zai kai Jauhar asibiti da wuri. A haka aka shafe kwanaki bakwai, amma Al'amin, yaƙi sakawa ransa cewa gaske ne ba mafarki ba. Kwanaki bakwan nan, babu wanda ya zo in da yake, ba wai dan ba a samu masu zuwan ba, an hana kowa ganinsa. Liti da walid, da sauran jama'arsa babu irin sintirin da ba su yi ba, amma aka hana su ganin sa. Mutuwar jauhar, ta karaɗe kowane gidan jarida, unguwanni zuwa gidaje. Abbu yayi kuka tamkar zai yi hauka, yayi dana sanin kasancewar sa mahaifin Al'amin. Gidansu jauhar kuwa, ba su san sun yi rashi ba, sai da aka tabbatar da mutuwar jauhar, kowa kuka da zubar da hawaye. Abbu yana kuka, ya sanya gwiwoyinsa a ƙasa, yana roƙon Baba ya yafe masa, da ya san Al'amin zai kashe masa 'ya, ba zai yarda a aura masa ita ba. Baba ya girgiza kai ya ce "Alhaji Ibrahim, ni wallahi haryanzu ban ji na yadda Al'amin zai kashe mini 'ya. Akwai abun da ya faru ni ban yadda shi ya kashe mini jauhar ba" Abbu ya ce "Wace hujja kake nema ko shaida bayan wannan? Ni na haifi Al'amin, kuma kowa ya san yana ta'amalli da miyagun ƙwayoyi" Cikin kuka mama ta ce "Yaron nan ya cuce mu, bai yi mana adalci ba, haihuwar ɗa irin jauhar a gidan nan, daga kanta an gama, ba ayi ba, kuma ba za ayi ba" Hafsa ta girgiza kai ta ce "Baba nima ina bayan maganarka, ƴan kwanakin nan, ina zuwa gidanta sosai da sosai, ina haɗuwa da shi, ita take bani labarin galabar da ta ci a kansa, da bani misalai daban-daban da aurenta. Son da yake nuna mata a gabana ba ya jin kunyata ko nauyina, suna matuƙar ƙaunar junansu. Har take gaya mini na tayata da addu'a, yanzu sigari ce kawai damuwarta da shi, har sai da na ji raina ya biya, da irin kalar soyayyar da suke yi wa junansu, dan haka gaskiya ban yadda mai zamani zai kashe jauhar ba, mutumin da idan zata fita baya nan, yake sawa ana bibiyarta dan kar wani ya kawo mata farmaki, mugwayen karnuka ya ajiye a layinsu, suna gadinta lokacin da yayi tafiya, duk dan kar a taɓa ta, gaskiya ban yadda ba". Anty ma tana kuka ta ce "Babu abun da mai shaye-shaye ba zai iya aikatawa ba, dan haka ba abun mamaki bane dan an ce ya kasheta, Allah sarki jauhar wannan wane irin mummunan ƙarshe ki ka yi?" A fusace Saifu yana kuka ya ce "Kar ki sake aibata mana gawar jauhar, wallahi ba ta yi mummunan ƙarshe ba, ta bi Allah, ta yi wa iyaye biyayya, ta yi biyayyar aure, idan ana nuna ɗan aljanna a duniya to jauhar ce, koma wane irin mutum ne shi, ai ku kuka yi bita da ƙullin da ta aure shi, kuma wallahi Allah ba zai bar kowane azzalumi ba, ita ta mutu ta huta". Haka aka din ga musayar yawu, har sai da Baba ya tsawatar tukuna. Da taimakon Naja'atu Bunkure, suka haɗa kai da lawyoyin gwamnati, Indabo ya cika su da kuɗi, har da alƙalin kansa. Domin tsayawa tsayin daka wurin tattara shaidu da hujjoji. Haka zalika ta fito ta bayyanawa duniya cewa, zata tsaya tsayin daka, har sai ta ga abun da ya ture wa buzu naɗi, sai an bi wa jauhar hakkinta, na kisan gilla da viper ya yi wa jauhar, mussaman dama ya riga yayi suna a harkar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi da kuma harkar daba. Ranar fara shari'a, haka aka zo da mai zamani a cikin sarƙa, yana ɗingisa ƙafa, saboda azabar da ya sha a hannun 'yan sanda, a kan ya amsa cewa shi ya kashe jauhar. Aka fara gabatar da shari'a, wani lawyer ya gabatar da kansa a matsayin wanda zai kare Al'amin, bai taɓa ganinsa ba, sai ranar a cikin kotun. Aka gabatar da charges ɗin da ake yi wa Al'amin. Ɓangaren tawagar lauyoyin gwamanti, da su Naja bunkure, suka din ga gabatar da shaidun bogi, suka kawo ƙwayoyin da suka samu a gidan Al'amin, tare da kawo bayanan likita, na cewa dukanta aka yi har ta kai ga rasa ranta, da abun da yake cikinta. Abun bai tsaya a nan ba, sai da aka kawo malam lawan, bayan shaƙa masa wasu muhimman kuɗaɗe, ya zo ya bayar da shaidar Al'amin ya saba dukan jauhar, idan ya je ya sha ya bugu, haka za su yi ta jiyo ihunta yana dukanta, a ranar ma sun ji kukanta, sai dai ba su yi zaton zai kasheta ba. Muryar Liti ce ta dawo da Al'amin hayyacinsa, dan duk surutan da ake yi, bai san me ake cewa ba. "Ƙarya kake yi dan ubanka, Viper ba ya dukan yar madara, ba ita ba kowace mace ma baya duka, a matsayin ku na maƙota idan yana dukanta, meyasa baku kai wa yan sanda ba, ƙarya kake maƙiyin Allah la'ananne, Viper ba zai taɓa cutar da matarsa ba, ba shi ya kasheta ba" jami'an tsaro suka yi waje da liti. Sai dai wani irin ihu da Viper yayi, sai da wasu suka fara gudu, ya daki katakon gabansa da ƙafarsa ya ce "Ƙarya ne, jauhar tana nan a raye, gobe zata haihu, matata  bata mutu ba" Da ƙyar aka danne shi, Alƙali ya aika shi gidan prison, tare da ɗage shari'ar. Haka ya cigaba da buge-buge, tamkar zai jefar da motar gidan yarin, sai da suka sumar da shi, sannan suka samu nutsuwa. Tun daga wannan ihun, bai sake magana ba, ba cin abinci, sai dai zai yi salla kawai. Har aka yi zama na biyu a kotu, bai ce uffan ba, duk wasu hujjoji Bunkure ce ta samar da su, lawyern gwamanti gabatarwa kawai yake yi. Sai dai juyin duniya, ya yi magana, yaƙi yi. Bunkure ta je gaban Al'amin ta tsaya ta ce "Amsa ɗaya kawai kotu take buƙata daga bakinka, kai ka kashe matarka jauhar?" Ya ƙura mata rinannun idanunsa, ta din ga yi masa wani irin kallo, mai cike da rainin wayo. Ya jinjina mata kai alamar eh. A nan suka buƙaci a ƙarƙare shari'ar, ba tare da wata huɓɓasa ba, lawyern Al'amin, ya ce ya yarda da duk abubuwan da masu gabatar da ƙara suka gabatar. Daga haka aka sake ɗaga shari'ar zuwa wata guda. Wata gudan da sai da ya shafe shekaru biyar a prison, ba a cigaba da shari'ar ba, ba kuma a sallame shi ba. Kullum burinsa shi ne ya farka daga mafarkin nan da yake yi, shi dai ya san matarsa na raye, ba ya cin abinci baya iya bacci, ya koma tamkar mahaukaci. Sai dai lokaci zuwa lokaci yana yi musu ihu, da kiran matarsa, ya kan kira sunan madaki da Indabo. Lokaci lokaci, ya kan ga aiken abinci, hakan ya sanya ya ƙara sakankancewa jauhar ce ke yi masa aike, bai sake ganin wani yazo wurinsa ba, tsawon shekaru biyar ɗin nan. Rana tsaka aka ce masa ya fita ya tafi gida an sallame shi. A ƙofar prison ɗin ya tsaya, yana tuna lokacin da ta zo tafiya da shi, lokacin da aka rufe shi, aka ce an kama shi da cocaine. Bai tsaya ko ina ba, sai unguwarsu, da ƙafa ya taka ya tafi, amma ya tarar da gate ɗin a rufe. Sai yayi tunanin ta koma gida ne, dan haka sai ya fara tafiya gidansu, dan tabattar wa. Gidansu ya fara zuwa, rahila da yaranta, gaba ɗaya suka dare, suka gudu ɗaki tana ihu ta ce "Ka fita ka kore shi, gashi can an sako shi, Allah wadaran yan siyasa, sun sako masifa da annoba, wanda bai san halacci ba". Abbu ya fito ya kalli Al'amin, ya koma kamar wani mahaukaci, a gigice ya nufo Abbu ya ce "Abbu, ina jauhar? Ta haihu ne? Ina abun da ta haifa?" Abbu ya ja da baya ya ce "Kar ka matso kusa da ni, Jauhar tana gidan uwarka da ubanka, dama ka gaya mini zaka kasheta, kuma ka cika alƙawarin ka Al'amin, na gode da muguwar sakayyar da ka yi mini, da ɓata mana sunan zuriya. Ka fita babu ni babu kai, ka nemi wani uban bani ba, na sallamawa duniya kai, ba zan cigaba da rasa makusantana, mutanen da nake ƙauna ba saboda kai, ka je na yafeka a duniya" "Na ji na yadda, amma ina jauhar? Sun ce idan na ba su abun da suke so, zasu kai ni in da take" "Sai dai ka bita kabari ka ɗauki ɗan naka, mara mutunci, ka fita ka bar mini gida, bana ƙaunarka bana ƙaunar ganinka" "Ba zai yiwu ba, wallahi sai kun fito mini da matata" ya juya ya fita da gudu, ya tafi dabar su, incomplete building ɗin da suke zaman shaye-shaye. Su Walid suna ganinsa, suka rirriƙe shi suna kuka, ya watsar da su ƙasa, ya ce "Walid, ina jauhar? Na san ta haihu ko?" Walid ya tashi tsaye ya ce "Viper ka nutsu mana, ya aka sako ka ne? Ba yadda bamu yi ba, a ƙarasa shari'arka mu ɗaukaka ƙara aka ƙi" "Dalla ina tambayar ku, ina jauhar, ko ta koma gidansu, ku bani kaya na canza na je wurinta, na san hanata ganina aka yi" Hawaye na zuba a idon liti ya ce "Viper, Ƴar madara fa ba ta raye, ta rasu" Al'amin yana zuwa nan a maganar, yayi shiru, yayi fatali da kayan gabansa, ya fara wani irin haki, yana nema ya kurma ihu. Nabila tana kuka, ta toshe masa baki tana girgiza masa kai. Ya saka hannu, ya cire hannunta daga bakinsa ya ce "Ban cancanci na haukace ba? Ban cancanci na nemi fansa ko ta wane hali ba kenan?" Nabila ta girgiza masa kai, kuka ya hanata magana. "Na kashe matata, ni na kashe jauhar ɗina, halittar da ta nuna mini tsantsar so da ƙauna" "Ba kai ka kasheta ba" Cikin tsawa ya ce "Ni ne, ni na kasheta. Meyasa da Abbu ya ce mini zai yi mini aure, na ce zan kasheta, ya ce mini Allah ya taimaka? Meyasa na kasa tuba na daina bangar siyasa da daba, a lokacin da zabra take ta ankarar da ni illarta, mai yasa sakamakon laifina ya faɗa kan matata?" "Astagfirullah, Viper kar ka yi saɓo" "Meyasa ban karɓi ƙaddarata ba tun da farko, na furta idan aka yi mini aure zan kasheta? Meyasa na jinkirta barin aikata laifi, sai da na rasa mutane masu muhimmanci a sanadin daba da shaye-shaye. Daba da bangar siyasa ta yi mini mummunan tabo, na kasa zubar da hawaye ko sau ɗaya tsawon shekarun nan, meyasa ba zan haukace na huta ba. Ina son matata, laifina ya shafe ta, ba ta ji ba bata gani ba, na kasa yadda ta mutu, haryanzu ina ganinta ina ganin ɗana a jikinta. Ko ban ɗauki fansa ba, ina fatan na haukace, ko na bita na huta. Ina ma jauhar ba ta sanni ba, da yanzu tana nan tana rayuwa cikin farin ciki, bani da sa'a ko kaɗan a rayuwata, duk wanda na saka sonsa a raina, sai Daba da bangar siyasa tayi masa illa" Huci yake yi, idanunsa suka rine zuwa ja mai ban tsoro. Ta sake mayar da hannunta bakinsa, ta rufe masa, tana kuka ta fara furta "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Astagfirullah wa atubuilaihi" A hankali ya fara maimaitawa shi ma, jikinsa na kyarma, kamar wanda ake kaɗawa gangi. Nabila ta ce "Ka yi i ajiyar zuciyan da kake dannewa" ya kama ɗaya hannun nata, ya ɗora saitin zuciyarsa, yana wani irin haki, wani irin bugu zuciyarsa take yi mai ban tsoro. A take ya saki wata irin nannauyar ajiyar zuciya, tare da hawayen da suka maƙale a tsakiyar zuciyarsa tsawon shekaru shida! Ayshercool 08081012143 58 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin matsanancin tashin hankali, Nabila tana kuka ta ce "Viper zuciyarka fa, dan Allah ka nutsu zata daina aiki, idan ta cigaba da bugawa a haka, ka cigaba da istigfari da maimaita Innalillahi wa Innalillahi raji'un" tayi maganar cikin damuwa, ƙara danna hannunta yayi a kan ƙirjinsa, yana wata irin shaƙuwa mai haɗe da haki, numfashin sa na fita sama-sama. A jejjere zuciyarsa take bugawa da ƙarfin gaske. Cikin tausayawa take kallon sa, Al'amin yana buƙatar kafaɗar da zai kwanta yayi kuka, babu wanda ya fuskanci ainihin matsalar sa, kowa ɗora masa laifi kawai yake yi, iftila'in da ya faɗa masa, kowa ya dare ya bar shi, sai abokansa duk da suna iya ƙoƙarin su a kansa, amma ba abun da yake buƙata suke yi masa ba. Ji tayi ina ma tana da damar, da zata rungume shi, ta bashi dama yayi kuka yadda yake so, ko zai samu afuwa a zuciyarsa, tsawon shekaru shida, yana dakon baƙin ciki da damuwa, kuma ya kasa zubar da hawaye sai a wannan lokacin. Haka yayi shiru ya sunkuyar da kai, sai dai bai saki hannunta ba, hawaye ne kawai yake zuba daga idonsa, taya shi take yi, sai dai ta rasa me ma zata kuma ce masa, a tsorace take da kar zuciyarsa ta buga. A hankali ya saki hannunta, ya goge hawayen sa, ya tashi zumbur, ya tattare kayan  ya mayar ɗakin, hatta kayan jauhar suna nan, lokaci lokaci, su Walid ne ke zuwa su karkaɗe gidan su share, dan idan ya bushi iska yana zuwa cikin dare, yayi ta tuna irin rayuwar da suka yi. Yanzun ma yana shiga ɗakin, ƙwaƙwalwarsa ta nuna masa ita zaune a kan gado, tana shirin dutse, gefe ga boti a kusa da ita a kwance, ya mimmiƙe yana ta goge jikinsa. Ta ɗago ta kalleshi tana murmushi ta ce "Manya gatan wasa, me ake so ne ake ta kallona? Ko fankar ce?" Tayi maganar tana kashe masa ido. Gadon ya nufa da hanzari ya kai hannu ya riƙe ta, amma ya ga pillow ne kawai a wurin. Ya dafe hannunsa a wurin, daga baya ya fito jiki a sanyaye ya ce "Mu tafi" Nabila ta saki niƙabinta tana ta kuka, suka nufi hanyar fita, ya gyara facemask ɗin sa suka fita. Yana fita yaga wasu daga magidantan layin, a ɗan tsaitsaye, suka yi ido huɗu da malam lawan, ya zura da gudu ya shige gidansa, ya rufe ƙofa. Ya danƙi hannun Nabila ya din ga sauri da ita, maimakon su bi titi, lunguna suka din ga bi, suna tafe yana haki, yana dafe ƙirjinsa. A dai-dai wata kan kwana, ya saki hannunta, ya danƙo wani mutum da yake zaune yana jin radiyo, yana cin karas, zuwa wani lungu. Nabila ta ce "Me yayi maka shi kuma?" Ya zaro iraƙi a ƙugunsa, ya saita masa a maƙoshinsa, ya ce "Bani wayarka" Jiki na rawa, ya ciro wayar, ya miƙa wa Viper. "Ka janye mini mutanenka, zan yi walƙiyya, idan ba haka ba, zan yi maka rami a maƙoshinka" Mutumin ya diririce, ya ce "Ban gane me ka ke nufi ba" Ya ɗaga mutumin ya haɗa shi da bango da ƙarfi, ya ce "Ka janye mini mutanenku zan tafi, idan na kuma magana, hanjinka zan naɗo da wuƙar nan" Mutumin ya ce "Ya aka yi ka gane ni, ka san identity ɗina?" "Saboda tsohon mai laifi ne ni, ba yau na fara aikata laifi ba" yana ƙoƙarin zira hannu a aljihu Viper ya riga shi, ya ciro bindigar da take aljihun mutumin ya ce "Ka yi abun da na ce, ko na harbe ka" A razane Nabila ta ce "Viper bindiga ce fa, dan Allah kar ka yi wani laifin mu shiga uku" bai kulata ba, ya sake saita mutumin da bindiga. Ya saka wayar a kunnensa ya ce "Zaku iya tafiya, we missed the target" ya katse wayar ya ce "Sai ka bani bindigata na tafi" Viper ya ce "Ɗaga hannunka, ka wuce mu je" ya tasa mutumin a gaba, tamkar ya kamo mai laifi, yana gana suna bin sa a baya, da ya motsa sai ya ji Viper ya ce "Idan ka waiwayo zan fasa kanka da bindigar nan" haka suka yi doguwar tafiya a haka, sai kuma ya ji shiru. Ya waiwaya, ya neme su ya rasa, a rikice ya bi hanya, saboda bindigar sa da take hannun Viper. Yana shan wata kwana, ya ga abokin aikins a tsaye da bindigar a hannunsa. "Gata, tun da ya ritsaka nake biye da ku, a hanya ya yar da ita, suka yi wani wurin, nayi ƙoƙarin bin su, amma ban cim musu ba". "Ohh shit, meyasa ba ka yi making wani move ba, wannan ai shirme ne kayi" "No, kar ka gargaɗe mu a kan haka, ka ce sai abun da ka ce, kai ka ke son ka kama shi da kanka" Ya fesar da iska ya ce "Kuma haka ne, amma gayen nan ya bani mamaki, na rasa ya aka yi ya gane ni a cikin fararen kaya. Kaga fuskarsa?" "A'a sir, fuskarsa a rufe take ai, ban ganshi ba, ni bayansa ma kawai na gani". "Na so naga kammaninsa, ko wataran zamu sake haɗuwa, suma informer's ɗin banzaye, da ba su sanar da wuri ba. Yi shiru ga oga Nasir yana kiran waya" Ya saka wayar a kunnensa ya ce "Hello sir" "Ya ake ciki ne?" "We miss the target sir" Nasir ya ce "Kamar yaya?" "Kafin mu je, ya bar unguwar, bamu tarar da shi ba" Nasir ya numfasa ya ce "Shikenan, ku dawo mu haɗu a office, sai mu sake shiri" "Ok sir" ya kalli abokin aikinsa ya ce "Mu je,ya ce mu koma office" Viper kuwa wata hanyar ya bi, suka ɓulla can wata unguwar daban. Sai dai suna tafe yana ta haki, yana haɗa hanya. "Viper mu tsaya ka huta, kalli halin da kake ciki, ko mu samu wani asibiti a duba ka, kar numfashinka ya ɗauke" bai ko nuna ya san da shi take ba, sai da suka fita titi ya saki hannunta ya ce "Ki koma gida" Cikin damuwa ta ce "To kai kuma fa?" "Ki tafi nace" yayi maganar da kyar, kawai ya tare wani mai napep ya shige ya tafi. Jiki a matuƙar sanyaye, ta koma chamber ta ɗauki motarta, ita kanta ta san ikon Allah ne ya kaita gida, amma kusan gaba ɗaya ba ta hayyacinta, tarin damuwa ce kawai cunkushe a ranta. Ba ta san yar madara ba, ba ta taɓa ganinta ba, amma ƙarshen labarin ya tsaye mata a rai, da wayonta ba a taɓa yi mata mutuwar da ta gigita ta ta ji ta ba, sai dai jin wannan mutuwar ta gigita ta, ta ɗaga mata hankali. A cikin zuciyarta take jin ƙaunar matar da ba taɓa gani. A wannan karon ma tayi kuka mai isarta, ga uwa uba, tausayin mai gayya mai aikn wato Al'amin, dan ita yar madara ta mutu ta huta, amma shi da blame ɗin ya dawo kansa, shi ne babban abun a tausayawa. Wayoyinta suka isheta da ringing, ta kashe su gaba ɗaya ta ajiye. Ta din ga fatan Allah ya mayar da Viper maɓoyarsa lafiya, dan ta tsorata da mummunan yanayin da ya shiga. Sannan haryanzu labarinsa da saura, ba duka bane ba, amma tana fargabar sake matsa masa son jin ƙarashen labarin, dan gudun kar ya sake shiga mawuyacin hali kamar yau. Tana ta saƙe-saƙe, sumayya ta yi sallama, ƙasa-ƙasa ta amsa, sumayya ta shiga ɗakin tana mita. "Malama kin ce mini zaki zo, amma kin shanya ni, bayanai ne suke ta fitowa a kan mutuniyar ki, ina son ki gana da mutanen direct, na haɗa ku, amma ki ka ƙi zuwa" Ji tayi Nabila tayi mata shiru, ta ce "Arfa meyafaru ne? Kamar kuka ki ka yi fa" "Kuka nayi sumayya" Cikin rashin fahimta ta ce "Kukan me kuma? Ko duk a kan shari'ar ne?" "Sumayya komai ma, yakamata nayi kukan ne kawai" "Arfa yakamata fa ace kin san kin girma, haba abu kaɗan sai kuka, ki din ga miƙa wa Allah lamuranki mana haba Arfa". "Arfa, Arfa" suka jiyo muryar Nasir yana ƙwala mata kira. Tayi shiru bata amsa ba, ya shigo ɗakin, ya tarar da ita a zaune, ta jingina da gado. "Ina magana ki ka yi mini shiru?" Ta ce "Kaina ne yake yi mini ciwo" Sumayya ta ce "Yaya ina wuni?" Ya amsa da "Lafiya ƙalau sumayya, ya aiki?" "Alhamdilillah" Ya sake mayar da idonsa kan Nabila ya ce "Waye mutumin da ya zo wurinki ɗazu a Office ɗin ki?" Ta ɓata fuska ta ce "Na gaya maka client ɗina ne ai" "A'a arfa, na tambayeki wani irin case ne zaki tsaya masa, kin ce is confidential ban san lokacin da muka fara ɓoyewa juna abun da ya shafe mu ya shafi aiki ba. Mutumin nan yayi kama da masu aikata miyagun laifuka, duk da ban ga fuskarsa ba" Ta girgiza kai ta ce "Allah ya kiyashe ni hulɗa da masu aikata laifuka, sai dai ko da mai laifin ne, a matsayina na lawyer babu ruwana da laifin sa, zan bashi kariya ne kawai. A wurinku ne ku ke kama mai laifi, a wurin lawyer babu ruwansa da mai laifi ko akasin haka, client ɗinmu ne a gabanmu ba laifinsa ba". Ya tsaya yayi shiru yana kallonta "Ban gane me ki ke nufi ba" Tayi murmushi ta ce "Ba wani abu da nake nufi yaya, aikinku kamo mai laifi, mu kuma namu aikin binciko gaskiya komai ɗacinta" Ya jinjina kai ya ce "I see, ɗazu informer's ɗin mu sun sanar da mu Viper ya je gidansa, da shi da wata da ba a san ko wacece ba, sai dai kan jami'anmu su je, ya bar unguwar" duk da ƙirjinta yayi dumm. Amma cikin iya siyasa ta ce "Ikon Allah, lallai wannan Viper akwai shu'umi, ya cika macijin gaske, wato lokacin da ya ga dama, sai ya baro raminsa ya fito shan iska, to Allah ya shirye shi. Amma ya batun abokinsa da kake bibiya?" Nasir ya ce "Nothing much, ya daina zuwa unguwar ma kwata-kwata, abun har mamaki yake bani, da mun hari wani abu da muke son mu kama shi, sai abun ya kuɓuce mana, amma muna nan muna ƙoƙari" Nabila ta ce "Gaskiya abun da mamaki, Allah ya yi jagora" Ya amsa da "Amin, Sumayya ki din ga yi wa yar uwar nan taki faɗa, bata ji ko kaɗan tana neman zunguro mana sama da kara, kasadarta tayi yawa sosai" Sumayya ta ce "Ana yi mata fa yaya, ka san halinta da kafiyar tsiya ne, amma zata daina in sha Allah" Ya jinjina kai ya ce "Allah ya sa" bayan ya fita Sumayya ta ce "Arfa, waye yaya yake magana a kai, ina fatan dai ba wani mai laifin bane ba, ko kuma wani abun ki ke shirin ɗaukkowa ba" Nabila ta kalleta ido cikin ido ta ce "Kina son na ce miki viper ne, ki je ki ji daɗin gaya wa waɗanda ki ke ba wa information a kaina?" Gaban sumayya ya faɗi ta ce "Information a kan ki kuma?" "Eh mana sumayya, ana bibiyata ta hanyarki, kina bibiyar duk activities ɗina kina sanar musu. To ki gaya wa ko suwaye suka saki, wallahi babu yadda suka iya da ni, gaba da gaba za su yi da ni, su karɓi abun da suke so daga wurina, ba wai su fake da ke ba kina ba su information a kaina ba" "Nabila waye ya gaya miki haka?" Nabila ta ce "Jira ki ke yi a gaya mini? Ni na ganoki, sai dai na kasa yadda saboda ƙauna ba ƙarya ce ba, kuma wanda ya gaya mini ba zai yi mini ƙarya ba, dan bai sanki ba, balle ya san alaƙarmu da ke. Please sumayya You can leave, ko ganinki ba na son yi wallahi" Sumayya ta ce "Nabila, ki tsaya mu fuskanci juna dan girman Allah" "Babu wata fahimtar juna da ta rage tsakanina da mai fuska biyu, ni da gaske na yarda da ke, ba zan bari a cutar da ke ba, mussaman ayi amfani da ni a cutar da ke ba, amma ke gashi ana ƙoƙarin cutar da ni ta hanyar ki. Koma waye yake bibiyar tawa, ki ce masa ya fuskance ni ya gaya mini abun da nayi masa. Idan kuma a kan ayyukan da na saka a gaba ne, babu wani mahaluki da ya isa ya hana ni abun da nayi niyya, ki tashi ki tafi" Sumayya ta miƙe tsaye, kawai ta ɗauki jakarta ta fita, tana tafe a hanya tana kuka, sam ba ta san da wasu kalamai za ta yi amfani ba, wurin fahimtar da Nabila ba, sai dai tayi mamakin gaske, a kan wanda ya gaya wa Nabila cewa ana bibiyar ta, da Nasir ne ya gaya mata, to da tabbas sai yayi zancen yanzu a gabanta, kuma sai ya tuhume ta, amma sai dai bai yi hakan ba. Bayan tafiyar sumayya kuwa, Nabila ƙanƙame pillownta tayi, tamkar ta samu viper, ta cigaba da zubar da hawaye. Viper kuwa a galabaice ya ƙarasa gidan da suke, gaba ɗaya nema yake ya fita hayyacinsa, haki kawai yake yi, zuciyarsa na cigaba da wannan matsanancin bugun. Ɗan mama ne kawai a gidan, ya tashi ya riƙo Viper cikin tashin hankali, ya shiga da shi ɗaki, ya kwanta a kan katifarsa, ya cigaba da ajiyar zuciya, yana haki, ga wani abu da yaƙi gaba yaƙi baya a tsakiyar ƙirjinsa. "Oga Viper, meyafaru ne? Baka da lafiya ne? Meyake damunka?" Ya jejjerawa Viper tambayoyin, amma babu guda ɗaya da ya iya amsa masa, ya lumshe idanunsa ya na ta sauke numfashi. Cikin sauri, ɗan mama ya kira Walid a waya, ya sanar masa halin da Viper yake ciki. Walid ya ce "Ka kula da shi, kar ka bari ya sake fita, gani nan zuwa" *** Madaki ne zaune a cikin dokar daji, a gaban wani mutum da shi da yaronsa lakwari. Ya miƙe ƙafarsa da ciwon jikinta yayi rami, mai zurfi, sai wani irin kore ruwa ne yake fitowa, wurin ciwon ya kumbura suntum babu kyawun gani ko kaɗan. Mutumin ya ƙare wa ƙafar kallo sannan ya ce "Ya riga ya yi maka illa, tabbas yana da makarin asirinka, dan kuwa ya karya shi ɓara, wuƙa da kaifi, za su din ga tasiri a jikinka. Cikin tashin hankali da damuwa madaki ya ce "Yanzu babu wani abu da za ayi a kai, idan ya so a kuma bani wani asirin?". "Gaskiya babu, yanzu dai magani zan baka, aje a haɗa shi da diddigar maƙera, ka yi kwana arba'in ana sakawa ciwon, sai ya warke sai kuma mu ga da abun da zamu ɗora". Madaki ya yi shiru, saboda baƙin ciki, lokacin da aka bashi asirin, an tabattar masa da babu wani wanda yake da laƙanin karyewar asirin, sai shi wanda ya bashin, wanda yanzu ya mutu sai ɗan sa yanzu dan kuwa shi kansa ɗan ma bai san makarin asirin ba, dan haka sun yi mamakin yadda aka yi Viper ya samu. Sun kamo hanyar dawowa kano, madaki ko iya magana baya yi, babu tunanin da yake yi, da ya wuce wani mataki zai ɗauka a kan Viper, dan kuwa karya asirin nan, dai-dai yake da karya alkadarinsa baki ɗaya. Kiran P.A ne ya din ga shigowa wayar Madaki, sai da yayi da gaske sannan ya ɗaga, domin kuwa gaba ɗaya ransa a jagule yake saboda tashin hankali, da fargabar halin da zai shiga, idan aka fuskanci Alkadarinsa ya karye. "Madaki, ina ka shiga ne, yau kwanaki kusan huɗu wayarka ba ta shiga, distinguish ya bayar da muhimmin aiki da kai kaɗai ne zaka iya yin sa" Madaki ya yi ajiyar zuciya ya ce "Aikin menene?" "Idan kana gari ka shigo" Madaki ya ce "A'a, na ɗan yi wani balaguro ne" "Duk in da ka ke ka dawo, honorable ya matsa a kan lallai a kama viper, yarinyar nan yake so a ɗaukko masa" Madaki ya ce "Wace yarinyar kenan?" "Wata lawyer ce, wadda na fara yi maka zancen nan" Madaki yayi wani huci, ya ce "Bari na shigo garin, zan yi maka magana" P.A ya ce "Wai madaki lafiya kuwa? Kamar ba ka da karsashi, meyake faruwa ne?" "Basar ka ɗauke tunaninka a kan hakan, zan faso idan na shigo gari" ya katse kiran yayi shiru yana tunani, tabbas ta bakin Al'amin daga lokacin da suka ga ya daina yi musu amfani zasu watsar da shi. *** Nabila ta kira layin Viper ya kai sau biyar, dan ta ji halin da yake ciki, amma ba a ɗagawa, har ta fitar da ran zai ɗaga ta ji an ɗaga wayar. "Haba master, ka barni cikin zullumi da tunanin halin da kake ciki,  ka ƙi ɗaga wayata". "Walid ne" "Oga walid, yana ina dan Allah?" "Gashi muna ta fama, jiki ya rikice gaba ɗaya". Cikin tashin hankali ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wani abun ne ya same shi ne?" "Ke zamu yi wa wannan tambayar, dan babu yadda bamu yi da shi ba, ya ce sai ya fita, wurinki zai zo, zai yi wani aiki, mun yi iya ƙoƙarin mu mu hana shi, amma ya ƙi saurarenmu, ko kin yi masa wani abu ne ki gaya mana dan Allah" "Wallahi Allah kenan, ban yi masa komai ba, office ɗina ya zo ɗazu.... Walid ya katseta ya ce "Office kuma? Ya ce kiranki zai yi a waya ku haɗu" "A'a zuwa yayi, yayi amfani da wayata da computer ta ta, daga nan ya ce zai ƙarasa mini labarin da ka fara bani, har gidansa muka je" ta yi wa walid bayanin yadda aka yi. Walid ya ce "To ki tayamu addu'a, jiki ya rikice, ɗan sakewar da yayi kwana biyu, ta gushe ya koma yadda yake a da. Salla kawai yake yi a kwance tun da ya dawo, sai dafe ƙirjinsa yake yi yana haki". "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Oga walid da ka ƙarasa mini labarin nan, duk da haka bata faru ba, da na san halin da zai shiga kenan, da ba zan takura masa ya gaya mini ba. Ubangiji Allah ya kawo masa mafita, Allah ya bashi lafiya, ba zai yiwu na fito yanzu ba, dan Allah ku kula da shi sosai. Zan zo in ga jikin nasa in sha Allah" "Shikenan, Allah ya kawo ki" ya kaste wayar, yana kallon in da Viper yake kwance, hannunsa ɗaya a kan ƙirjinsa, yana ta sauke numfashi. *** Duk wasu kalamai da Abdul yake tunanin idan yayi amfani da su, zai shawo kan ramma, yayi amma fafur taƙi saurarsa, ya kaɗa ya raya, amma taƙi saurarsa. Da ya addaba mata cikin tsawa ta ce "Wai me kake so ne Abdul, ai ban yi zaton mugun zaluncinka ya kai haka ba, ka yi mini fyaɗe an ɗora wa mutanen da suka taimaka mini sharri, wannan wace irin rayuwa ce?" Ya sake kwantar murya ya ce "Ki fahimce ni dan Allah, zan yi duk iya ƙoƙarina a kan mutumin nan ya fita a sake shi, dan Allah ki daina ɗaga hankalinki" "Dama dole ka ce haka mana, tun da kana ganin ko ta halin ƙaƙa, kuɗi zasu ƙwatar maka komai, baka tunanin mawuyacin halin da zaka jefa zukata, baka yi dacen hali ba ko kaɗan" taƙi sauraronsa, sai uban miyagun maganganu da ta din ga yaɓa masa. *** Bacci ya gagari idanun Nabila, ta ga tamkar an ƙara wa daren tsawo, gashi ta kasa bacci, ƙarshe ta tashi tayi alwala ta tayar da nafila. A gaggauce ta hana baba magajiya aikinta, ana idar da sallar asuba, ta shiga kitchen ta dafa abun da take buƙata, da duku-duku, ta ɗauki motarta ta fita. Jin ƙarar mota ya sanya Nasir ɗaga labulensa ya duba, ya ga babu motarta, ya kalli agogo, hari sam bai gama waye ba, ya fara tambayar kansa ina tafi da wannan duku-dukun?. Gudu ta din ga yi a titi, gani take yi tamkar kafin taje, wani abun ya same shi. Gari yayi haske sosai tana hanya, ta ajiye motarta a wani wuri, ta fito ta tsaya ko zata samu abun hawa, amma bata samu ba, dan haka ta cigaba da tafiya da ƙafa, gabanta na ta tsananta faɗuwa sai addu'a take yi. Ta sha tafiya sosai, sannan ta samu abun hawa ta hau, ya ƙarasa da ita. Kasancewar da tafiya daga titi zuwa gidan da yake, haka ta din ga haɗawa har da gudu, har ta ƙarasa tana ta haki, ta shiga da sallama, ta ƙarasa ƙofar ɗakin, ɗan mama ta hango zaune a gaban Viper, yana ta rarraba ido, daga shi sai shi a gidan. Ƙwayoyi ne a hannun Al'amin, gefe ga allura a cikin sirinji, amma sai haki yake yi mai ban tsoro. Da sauri ta ƙarasa ɗakin, tana cewa "Wannan ƙwayoyin na menene?" Kafin ta ƙarasa ya watsa su a bakinsa, babu ruwa yake ƙoƙarin haɗiyewa, ba ta san lokacin da cikin tsawa ta ce "Viper meye haka? Ƙwayoyin meye wannan kashe kanka ka ke son ka yi?" Bai kulata ba, ya cigaba da ƙoƙarin haɗiyewa, sai dai ya kasa saboda abun da yake ji ya tokare masa a wuyansa zuwa ƙirjinsa. Matse bakinsa tayi iya ƙarfinta, tana girgiza masa kai "Kar ka haɗiye, wallahi hakan ba mafita ba ce ba, dan girman Allah ka zubo su daga bakinka" hankaɗeta yayi yana ta huci. Ɗan mama ya ce "Ki daina zuwa in da yake, zai yi miki illa, wallahi aiken su Walid yayi, ni kuma yayi mini barazana da wuƙa, na samo masa kuma wanda ya watsa a bakinsa sun yi yawa, sun yi masa ƙarfi" "To waye ce ka kawo masa, ba sai ka gaya wa Oga walid ba, ai ka san ba zai taɓa iya kisan kai ba" Ta sake tunkarar Viper, sai haki yake yi mai haɗe da huci, tamkar kumurcin, yana motsa bakinsa a hankali, yana son haɗiye ƙwayoyin. Bakinsa ta sake matsewa, idanunsa sai buɗewa suke yi suna lumshewa, wanda suka fara narkewa a bakinsa, sun fara rikita masa lissafi. "Kalleni nan, ka fito da su na ce" tayi maganar tana zare masa ido. Ya ɗago a hankali ya kalleta, ta ce "Ka zubo da su, kar ka haɗiye. So kake ka kashe kanka, idan ka kashe kanka, ɗan wuta zaka mutu, kuma ko ka je lahira ka mutu ɗan wuta, yar madara kuwa muna saka mata ran tana aljanna, kaga ba zaka ganta ba" A galabice, ya buɗe bakinsa, yana zubo da ƙwayoyin da suka rage a bakinsa, yana ta haki. Shammatarta yayi, ya ɗauki sirinjin da yake gefensa, ya caka mata a hannunta, wata irin ƙara tayi, cikin razani, dan ba ta yi tsammanin hakan ba. Ɗan mama ya rikice, ya nufo su da sauri, Viper ya kalli in da ya caka mata sirinjin, ya kalli fuskarta yadda ta fara kuka, sai kuma ya ankare da abun da yayi. Sai ya rikice, ya zare sirinjin ya jefar ya riƙeta ya ce  "Zahra, me nayi miki? Yi haƙuri, na daina shan komai, ai nayi miki alƙawari" yayi maganar yana ƙoƙarin kai hannunsa fuskarta, ya share mata hawaye. Walid ne suka shigo tare da liti, suka nufo su, liti ce wa yake "Me ki ka yi masa?" Viper ya yinƙura ya tashi, amma ya yanke jiki ya faɗi. Suka rufu a kansa, suka ɗaga shi da kyar, Nabila ta gaya wa Walid a halin da ta zo ta same shi. Walid ya kalli ɗan mama, cikin tsananin ɓacin rai, ɗan mama ya ce "Nifa bani na kawo masa ba, wallahi ɗaukko masa kawai ya saka nayi, ban san a ina ya samo abun sa ba" Suka mayar da hankali a kan Viper, sai dai ba maye kawai yake yi ba, suma yayi, ga numfashinsa iya ƙirjinsa yake. Nabila ta ce "Dole fa a kai shi asibiti, ko da hakan yana nufin a kama mu ne baki ɗaya, lafiyar sa ita ce mafi muhimmanci a wannan lokacin" Walid ya ce "Haka ne, amma wani asibiti zamu kai shi?" Liti ya ce "Akwai wani asibiti a can bayan gari sosai, sai dai na kuɗi ne, ina ga kamar can zai fi zama safe" Nabila ta basu mukullin motarta, ta gaya musu a in da take. Liti ya karɓa ya tashi ya fita. Nabila kallonsa take cike da tausayawa, namijin gaske ne, sai dai ta wata fuskar yana da raunin zuciya sosai. Da liti ya kawo motar, suka yi kama kama, suka ɗauke shi, suka shafo tafiyar nan da shi, suka fito titi. Liti ne yake jan su a motar, ɗan mama da Viper da walid suna baya. Asibiti ne mai kyau, sai dai ya yi nisa da gari sosai da sosai. Ganin halin da yake ciki yasa suka karɓe shi da gaggawa, Nabila ta tambayi ya tsarin Asibitin yake, da payment ɗin, aka ce su bari, a fara ceto ransa tukuna. Da aka tambayi sunan Al'amin, sai Walid ya ce "A saka masa Muhammad Nura" Liti ya ce "Meyasa baka bayar da normal sunansa ba" Ya bashi amsa da "Saboda tsaro" A kan oxygen aka fara ɗora shi, saboda numfashinsa, sannan aka fara sauran ƙoƙari a kansa. Walid kallonta kawai yake yi, yadda take a rikice cike da tashin hankali, babu ma alamar tana fargabar a kamata ko wani ya ganshi, ta uzzurawa likita da tambayoyi. Likitan yayi mata bayanin yadda Jinin Al'amin ya hau, ga bugun da zuciyar sa take yi, fiye da kima kamar yadda ECG ɗin sa ya nuna, he's at very risk of having heart attack. "Subhanallah, dan Allah doctor kayi ƙoƙarin ka, na san Allah ne mai komai, amma dan Allah ka taimaka" "In sha Allah zamu yi iya a ƙoƙarin mu a kai" Tayi masa godiya, ta tafi reception ita da litu, suka gaisa da cashier ta tambayi, me za su yi depositing, na patient ɗin su da aka yi admitting?. Ya tambayi sunan mara lafiyan, liti ya gaya masa, ya duba cikin system ɗin gabansa ya kalle su ya ce "Ai an biya" Suka kalli juna da ita da liti, liti ya ce "Malam ka duba sosai, ɗazu muka shigo fa, aka ce mu bari a fara bashi taimakon gaggawa, ka duba ko masu irin sunan biyu ne". "Shikaɗai ne me irin sunan da aka yi admitting yau, Al'amin Ibrahim" Suka kalli juna da Nabila, liti ya ce "Mu sunan mara lafiyanmu Muhammad Nura" "Wanda ya biya kuɗin, sunan da ya bamu kenan, ba shi ne na ɗaki mai lamba 2 ba? Al'amin Ibrahim ya ce mana, ya turo kuɗi ya ce ayi masa duk abun da yakamata". Ayshercool 08081012143 59 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Nabila ta ce "Malam ya za ayi mu kawo mara lafiya, mu zo kuma ace mana wani ya biya  kuɗinmu, dama haka ake yi, wannan wane irin abu ne, ka gaya mana bills ɗinmu mu biya, mu bamu san kowa ba" Ya girgiza mata kai ya ce "No ma, ba zan karɓi kuɗinku ba, na gaya miki an riga an biya" "Waye ya biya?" Liti ya ce "Kai bana son nuƙu-nuƙu, wanene ya biya kuɗin?" "Nima ban sani ba, management ne suka turo mini receipt, aka ce kar mu karɓi kuɗinku, an yi settling bills ɗin" Nabila ta ce "Suwaye management ɗin?" Yayi shiru yana kallonta. "Malam kayi mini magana, ka tsare ni da ido, suwaye management ɗin? Suwaye suka biya kuɗin?" Liti ya ce "Ki yi magana a hankali, kar ki janyo hankalin mutane kanmu" Tayi ajiyar zuciya ta ce "Ana bibiyarmu, wanda yake wannan abubuwan ya san duk wani motsi da muke yi" Liti ya jinjina kai ya ce "Nima nayi wannan tunanin" Nabila ta ce "Mu koma wurinsa, kafin mu san abun yi" suka koma in da suka baro Al'amin da walid da ɗan mama. Walid na ganin su ya ce "Yaya? Nawa ne kuɗin?" Nabila ta ce "Kar ka damu, an biya" Tayi maganar tana zama a gefen Viper, ta tsurawa fuskarsa ido, kawai tuno yadda ya din ga kuka ta din ga yi, gaba ɗaya jikinta ya ƙara sanyi. Walid ya ce "Ba zaki ga likita ba, wurin da ya caka miki allura?" Ta girgiza kai ta ce "Bakomai, ni yanzu ta lafiyarsa nake yi" "Amma yakamata ki koma wurin aiki fa, ai muna tare muna kula da shi" "No, ko na tafi hankalina ba zai kwanta ba, ba zan iya aikin ba, bari na jira naga abun da hali zai yi" Likita ya sake shigowa, yana duba Al'amin. Ya ce "Alhamdilillah, ina ga ya samu bacci, dan ya farfaɗo daga suman" Nabila ta ce "Masha Allah" ji tayi ya taɓa hannunta, ta kalli hannunsa, ya yi mata alama ta matso. Ta matsa ta kai kunnenta saitin bakinsa, a hankali ya ce "Ki gaya masa a cire mini wannan abun na hancina bana so". "Haba master, baka ga yadda kake numfashi da kyar bane ba? Dan ya taimaka maka aka saka maka shi, dan Allah ka yi haƙuri ka ji, Allah ya baka lafiya" Ya sake cewa "Ki ce musu bana iya bacci, yayi mini abun da zan yi bacci, kaina zai tarwatse"ta ɗago ta kalli likitan ta ce "Doctor, ya ce dan Allah ayi masa allurar bacci, so yake yayi bacci baya iya bacci" Likitan ya ce "Ai mun yi masa, kuma da jinin ya sauka zak yi bacci mai yawa mai daɗi in sha Allah" Ta sake sunkuyawa, zata yi masa magana ya ce "Bana son baccin, ba na son jinin ya sauka, bani da rabon sake yin su, Allah ya nuna mini ranar da zan bi matata" Babu wanda yake iya jin abun da yake faɗa, sai ita, muryarta na rawa take yi masa magana a hankali cikin nutsuwa. "Haba Al'amin, mai babban suna, shikenan bawa ba zai yi imani da ƙaddara ba, tun da ka fuskanci kurakuran da ka yi a baya, ba sai mu nutsu mu nemi mafita ba, yanzu idan ka mutu maƙiyanka sun ci galaba a kanka kenan fa. Dan Allah ina roƙonka ka janye wannan fatan da ka ke yi, kuma in dai muna tare in sha Allah zaka yi bacci mai daɗi mai cike da nutsuwa da kwanciyar hankali trust me. Wallahi i feel your pain, bani na tsinci kaina a halin da ka ke ciki ba, but ina jin zafi a zuciyata, in sha Allah you won't cry alone, an cutar da kai, in sha Allah kuma sai in da ƙarfina ya ƙare a kan ƙwato maka hakkinka, in sha Allah sai nayi sanadin dawo da farincikin ka. Amma sai ka yi haƙuri, ka yi haƙuri, kayi haƙuri na san da wahala, da ciwo, an yi maka illa, amma ina roƙonka a wannan karon kar ka jinkirta tuba, mu yi ta addu'a, Allah ya taimake mu, ka kwantar da hankalinka ka yi haƙuri, Allah da kansa ya rarrashi masu haƙuri a cikin Alqur'ani" Yayi shiru yana sauraren Nabila, hawaye yana bin gefen fuskarsa. "Madam ya kuma kike kuka, mu da muke son hankalinsa ya kwanta, jininsa ya sauka?" Liti ya ce "Rabu da shi doctor, kukan shi ne samun afuwarsa, mun gode sosai da ƙoƙarin ku. Cikin kalaman hikima, da tausasawa, ta cigaba da yi wa Viper nasiha, tare da bashi ƙwarin gwiwa, a kan cigaba da haƙuri, da kuma Addu'a. Har bayan azahar, Viper bai gama frafaɗowa ba, haka Nabila ta haƙura ta tafi gida, bayan ta ajiye musu abincin da ta zo da shi. Sai magariba ta isa gida, Allah ya sa Abba baya nan, balle ta sha tuhuma. Message ne ya shigo wayarta, ta ɗauka ta duba. "Arfa dan Allah kar ki yi mini mummunar fassara, ki tsaya ki saurare ni mu yi magana, kin ƙi ɗaga wayata, hankalina a tashe yake, amma ki bani dama nayi miki bayani, dan girman Allah" Har jikin Nabila yayi sanyi, kamar ta yarda da maganar Sumayya, sai kuma ta fasa, tayi mata reply da "No peace for wicked person, kar ki sake tunanin zan yarda da maganarki" ta saka lambar a busy, ta cigaba da sabgar gabanta. Ta idar da sallar isha'i, tana zaune tana cin abinci, kawai Nasir ya faɗo ɗakin, babu ko sallama. Ta ɗaga kai ta kalle shi, amma bata ce masa uffan ba. "Arfa" "Na'am yaya" "Ina ki ka je yau?" Ta ɗaga ido ta kalleshi ta ce "Meyasa kake tambayata?" "Ki bani amsa kawai" Cikin ko in kula ta ce "Wurin aiki" "Ƙarya ki ke yi, me ya kai motarki hanyar ungoggo?" Ta ajiye cokalin ta ce "Haba DSP, mutum nawa ne suke da vibe a birnin kano?" "Ya ina magana kina nema ki raina mini hankali, wurin aikinki an ce baki je ba" "Amma yaya ka san aikina ba na zama wuri ɗaya bane ba, yaya ka ke yi mini tmbaya kamar ka ritsa ƴar ta'adda ne? Wataƙila harkar aiki ne ta kaini wurin, bibiyata kake yi kenan? Ko kuwa meyafaru ko rashin yadda ya shiga tsakaninmu ne?" Ya sauke numfashi ya ce "Gaba ɗaya kwanan nan kin canza Arfa, na je Division ɗin ungoggo kan wani case, a hanya na ga motarki, dan lambar motarki ce" "Abokin aikina ne ya ari motar, suka fita, ta sa ta samu matsala. Sannan kuma ni ban canza ba, kai ne dai ka canza mini kwanan nan, ni ban san me nayi maka ba, duk ka tsane ni, ka daina goyon bayan gaskiya, ni na fara tsoron ko kaima ka fara karɓar cin hanci" tayi maganar tana ƙaƙalo kukan kissa. Sai kuma ya kwantar da murya ya ce "No ki fahimce ni, ke ɗin ce yanzu dole sai ana saka miki ido, kar wani abun cutarwa ya samar mini ke, ki yi haƙuri ki daina kuka" a haka ya ɓuge da rarrashin ta, ta nuna masa komai ya wuce, yana fita tayi masa gwalo, tare da ajiyar zuciya. Ta ɗaukko wayarta ta ce "Bari na kira na ji ya jikin ɗan marayan zakina" sai dai wayarsa a kashe, haka ta haƙura. *** Gaba ɗaya ramma ta fita daga harkar Abdul, abun duniya ya addabe shi, gashi ya kasa gano in da mahaifiyar ta take, babban tashin hankalinsa kar ta gano cewar mahafiyarta ta ɓata. Dan bai san wane irin kalar bori zata yi masa ba. Ga Indabo ya uzzura masa, dan har an kai masa kuɗin aure, ga shirye shiryen takararsa na ta ƙara yin nisa, amma gaba ɗaya hankalinsa baya kan takarar. Abokansa sai mita suke yi masa a kan duk ya canza, ga aurensa an saka su fara shiri, amma ya kasa mayar da hankali a kai, sun kasa gane kansa gaba ɗaya. Babu wanda ya tsaya saurara da bashi amsa a kan surutun da yake yi. Yana zaune yana kallo, amma hankalinsa ba a kan kallon yake ba, tunani kawai yake yi. Ramma ta ƙaraso kansa ta tsaya, ya ɗaga kai ya kalleta, ya tashi zaune sosai ya ce "Rahama, ya aka yi ne?" Ta ƙaraso ta durƙusa a kan gwiwoyinta, hawaye na bin fuskarta ta ce "Abdul yasar, dan son da kake yi wa Allah da annabinsa, ka mayar da ni gaban mahaifiyata, naga message a notification ɗin ka, wai aure zaka yi, dan girman Allah ka mayar da ni wurin uwata da ɗan uwana, na yadda zan ƙarasa rayuwata, a rushen zan tattara ta na rayu, ba ma na saka ran zan zan yi aure, na yarda na rayu a haka" Ya kalli ramma ya ce "Daga ganin message sai ki ce aure zan yi? Bincike ki ke yi mini kenan? To ni ba wani aure da zan yi ". Cikin kuka ta ce "Ka daina yaudarata Abdul, ka rabu da ni, idan kana son iyayenka, na gaji, na gaji na gaji da haƙuri, da fatan zaka mayar da ni gida, ka ƙyaleni dan girman Allah, ai ka gama morar abun da kake so zuwa yanzu, kowace irin ƙishirwa ce ka kasheta zuwa yanzu ka rabu da ni dan Allah " tayi maganar cikin ɗaga murya. Abdul ya kalleta a tsanake ya ce "Kin manta alƙawarin da ki ka yi mini ne?" "Babu wani alƙawari da nayi maka, ni ban san wani alƙawari ba, ka mayar da ni gida" "Wallahi ƙarya ki ke yi ki rusa maganar da muka yi da ke, da alƙawarin da ki ka yi mini" "Ka yi mini duk abun da ka ga dama, amma ni dai ka sakeni na koma gida, idan duk matan duniya ne ka je ka aura, ban damu ba, amma a yanzu tun da dai ka gama da rayuwata dan Allah ka rabu da ni" Abdul ya tsura mata ido, yadda take kuka wiwi har da majina. Ya saukko daga kan kujerar, ya zauna a gabanta ya ce "Rahama kishina fa ki ke yi" Kamar zata kai masa mari ta ce "Ƙarya ne, Allah ya kiyayeni ya tsare ni da kishin ƙazamar halitta mara tsoron Allah kamar ka, ni kishin rayuwata nake yi" Ya sauke numfashi ya ce "Zan mayar da ke, amma sai kin cika mini alƙawarina, sannan kin haifa mini ɗa sannan zaki koma gida, kin ga idan kika haihu duk duniya babu wanda ya isa ya raba ni da ke" yayi maganar yana share mata hawaye. "Abdul ba zan taɓa yafe maka ba, na bar ka da Allah" "Duk cikin kishina ne, matsayin matar da zan aura daban, naki ma daban, you are like my guest house, wurin hutawa ta da nishaɗina" Jiki a sanyaye ta ce "Ka cuce ni Abdul, duk saboda ina 'yar talakan ƙauye, mara gata mara galihu" Ya girgiza mata kai, ya haɗe bakinsa sa nata, wata irin ajiyar zuciya take yi, a hankali ya cire bakinsa daga nata, ya kalli idanunta ya ce "Iya wuya rahama, ina tare da ke, ban ga wanda ya isa ya raba ni da ke ba. A lokacin da maza da yawa suke gudun matan da suka lalata, ni a dai-dai lokacin soyayyar yarinyar da na lalatawa rayuwa ta yi mini kamun kazar kuku". Jiki babu ƙwari ta cw "A hakan? Wace irin soyyaya ce zaka yanke mini farincikina ba tare da wani dalili ba, bana sonka Abdul ko kaɗan" "Ki saurari zuciyarki, kina jin zafin abun da nayi miki ne kawai, amma kina so na rahama, nima kuma ina matuƙar sonki" "Da ban yi wa kaina, da mahaifiyata adalci ba, idan na fara sonka Abdul yasar" "Zuciyar ki, cike da ƙuruciya, kina ƙoƙarin sakawa kanki ƙiyayyata ne ta ƙarfin tsiya ne". "Wallahi wannan ba so bane, ka gama lalata ni, ka samu abun da kake so, kuma ka ce sona kake, me yayi saura?" "Kin san abun da na ɗauko ki ki yi mini, kuma na daina kamar yadda ki ka buƙata. Wuri ɗaya nake kwana da ke nake tashi, amma na daure, ban sake yi miki ba, kuma na lazumci istigfari kamar yadda ki ka gaya mini. Kar ki saɓa alƙawarinmu mana. Wa ki ka taɓa ganin ya lalata yarinya ya bita kuma yana so? Ke kin san waye ni a garin nan da ƙasar nan. Na fiki shekaru, da ilimi da tarin dukiya, amma gaba ɗaya na bar abun da yake gabana na tattara hankalina a kanki, ki yafe mini mana sweetheart, ki yarda ki so ni, zan goge laifukana zan kuma mayar da ke wurin mama in sha Allah" "To yaushe?" "Very soon, da zarar kin yafe mini, kuma kin cika mini alƙawari" Ramma ta share hawayenta ta ce "Abdul ta yaya zan haihu da kai, in kalli duniya in ce musu me? Baga mata nan zaka aura ba, ba sai ku haihu ba?" "Naki nake so please" yayi maganar yana sumbatar goshinta, cikin tsananin so da shauƙinta. *** Yau ma uban sammako Nabila ta yi, ta tafi asibitin da Viper yake, sai dai ba ta ɗauki motarta ba. Yanzu ma ɗan mama ta tarar, yana ta sharar uban bacci, babu liti babu Walid. Viper kuma yana zaune, ya jingina da bango idanunsa a lumshe. Murmushi tayi, tare da farin cikin ganinsa a zaune. Ta ƙarasa ta zauna ta ce "Yallaɓai, good morning, ya jiki? Alhamdilillah na ji daɗin ganinka a zaune" sai dai kamar mai bacci, bai buɗe idonsa ba. Hannunsa ta kalla, ɗaya da drip, ɗaya kuma kamar lazumi yake yi. Wani irin farinciki ya kama Nabila. Wani baƙin abu ta hanga, a gefen pillown sa, ta saka hannu ta janyo, ta ce "Menene wannan, ko kayan da zaka canza ne?" Tayi maganar tana buɗewa. "Wannan rigarka ce?" Buɗe idonsa yayi ya kalleta, cikin wani irin zafin nama ya fizge rigar daga hannunta, ya hau waige-waige. Ta ce "Menene? Meyafaru?" Ya kalli in da ɗan mama ya saki baki yana bacci, ya kalli taga babu hanyar shiga ko fita ta tagar, ya sake ɗaga rigar. Baƙar riga ce shirt, mai ɗauke da hoton tambarin dragon a gefen rigar, bayanta kuma an rubuta wasu alphabets, da bai bar Nabila ta karanta ba. Duk da jikinsa babu ƙwari haka ya saka ƙarfin sa, ya yayyaga rigar, yana cigaba da waige-waige. Cikin rashin fahimta ta ce "Wai me yake faruwa ne?" Ya girgiza mata kai, ya sake jingina. Nabila ta kalle shi ta ce "Akwai damuwa fa, jiya an yi settling bills ɗin ka, sai dai bamu san waye ba, an ƙi gaya mana ko wanene" ya ƙura mata ido, ta jinjina masa kai, alamar da gaske take. "Dan Allah ka gaya mini, menene yake faruwa ne, bai kamata ka ɓoye mini komai ba, tare fa zamu yi gwagwarmayar nan" Sai ya lumshe idanunsa ma, yaƙi kulata. "Haba master, yar suganka ce fa, talk mana" a hankali ya fara kaɗa ƙafa, amma bai yi magana ba. "Sweetheart" ta faɗa tana dariya ƙasa-ƙasa. "Sweetheart magana nake fa" sai ya kwanta ya juya mata baya baki ɗaya. "Am sorry wasa fa nake yi maka, ya ƙarfin jikinka to, ina fatan akwai progress, kana samun sauƙi?" Ya girgiza kansa alamar "A'a" Ta ce "Ohh ni Nabila ina ganin mulki yau, Allah dai ya jaddada rahama da Fatima jauhar, ta yi ƙoƙari sosai" Ya ce "Amin" tausayin sa ne ya sake kama ta, ta ce "To tashi ka karya, na san yanzu za a zo yi maka allurai, kuma na san kana jin yunwa" Bai yi magana ba liti ya shigo da leda a hannunsa, ya kalli ɗan mama da yake ta bacci, ya dake shi da ƙafarsa ya ce "Tashi, ɗan asara, idan ma sace shi za ayi, kana kwance ka shanya baki kamar fatarin mata kana bacci" ɗan mama ya tashi yana mutsutsuka ido. Jauhar ta kalleshi ta ce "Ina kwana?" Ciki ciki ya amsa, ya dafa Viper ya ce "Maza ya ne, ya jikin?" "Alhamdilillah" "To masha Allah, ga brush ɗin da toothpaste, ka wanke bakin, yanzu Walid zai kawo abinci, sai ka yi wanka ka canza kaya" Ya yinƙura ya tashi zaune, ya ƙurawa ɗan mama ido, sannan ya ce "Kai waye ya shigo ɗakin nan jiya da daddare?" "Likita ne, sai mai bada magani Nurse, sukenan" "Ƙarya kake yi" Ɗan mama ya ce "Wallahi sukaɗai na gani" Liti ya ce "Dama ya kwanta yana ta uban bacci, ya za ayi ya san me ake yi? Ina fatan ba wani abun ne ya faru ba?" "Babu komai" Da Al'amin ya shiga banɗaki, sai Nabila ta fita tana waya da barrister Habib, ya ce lallai yana son ganinta, Sumayya T ladan ta turo wasu mata, kuma zasu taimakawa aikinta a kan bunkure. Nabila ta yamutsa fuska ta ce "Ka sallame su kawai, babu buƙatar na gansu" "Kamar yaya, abu mai muhimmanci da ki ke nema, ki ce a sallame su" "To ai nayi nisa ne, yaushe na bar abun da nake yi na zo" "Ki bari koma menene ki taho yanzun nan" to kawai ta ce masa, ta ajiye wayar. Ta cikin niƙabinta, take ƙarewa asibitin kallo, wurin cashier ta sake zuwa, sai dai yau wata mace ce. Suka gaisa Nabila tayi mata bayanin abun da ya faru jiya, ta buƙaci ta dubo receipt ɗin da aka turo musu na biyan kuɗin, ta ciro ta bata. Ta shiga computer ta duba, ta kalli Nabila ta ce "Ban ga receipt ba, kawai an saka bill settled" "Ina ne ofishin MD, ko admin na asibitin nan, dole fa a nemo wanda ya biya kuɗin nan" Ta ce "Ba sa shigowa da wuri, amma maybe zuwa anjima" Nabila ta juya ta koma ɗakin Viper. Ya canza kaya ya zauna a kan gadonsa. Har walid ma ya zo, ya buɗe masa wainar shinkafa ta sha ƙuli-ƙuli, yana lallaɓa shi ya ci. "Barrister har kin zo ashe?" Ta ce "Eh oga Walid, na zo tun ɗazu, naje likita ya duba ni, allurar da master ya caka mini jiya, hannuna ya sage" da sauri Viper ya kalleta. Walid ya ce "Subhanallah, Allah ya sauwwaƙe ya ƙara afuwa" Ta kalli wainar gaban Viper, ta ce "Oga walid ɗauke wainarka, na dafo masa abinci. Ta janyo ledar viva daga ƙarƙashin gadonsa, ta buɗe food plask, ta ɗaukko mini tea flask ɗin ta, ta haɗa masa tea. Faten dankalin turawa ne, ya sha ganye sosai da nama, sai ƙamshi yake yi duk ya cika ɗakin da ƙamshi. Ta miƙa masa shayin ta ce "Bisimillah ranka ya daɗe, kaga tea ne, da ɗuminsa sai ka samu cikinka ya warware, kaga tun jiya baka ci komai ba, ina fatan Allah ya baka lafiya da wuri, mu cigaba da aiki muna addu'a, in sha Allah sai mun dangana da nasara" Ya ɗaga kai yayi mata wani irin kallo, ta ce "Ba danni ba, dan Allah idan baka ci ba ba zan ji daɗi ba, dan kai na girko na kawo maka. Lafiyarka na da matuƙar muhimmanci a wurina please mana, ka karɓa" ya miƙo mata hannu, ta saka masa kofin tana kallonsa tana murmushi. "To yi bisimillah ka fara sha". Ɗan mama ne yake ta ƙoƙarin yin dariya, amma yana jin tsoro, ganin yadda aka bar Walid da busashshiyar wainarsa. Liti kuwa ƙyaƙyatawa ya din ga yi ya ce "Walid, miƙo mana wainar nan, mu ƙaddamar mata" "Sannu maye, aikuwa ba zaku ci ba, ku ci kanku" Nabila murmushi ta yi, ta cigaba da yi wa Viper hira, cike da tausayawa, da bashi ƙwarin gwiwa a kan haƙuri da ƙaddara. Sannu a hankali yake cin abincin, har ya cinye tas, ya shanye shayinsa. Wani murmushin ta sake yi masa, ta ce "Alhamdilillah ala kulli halin. Allah ya ƙara maka sutura da ingantacciyar lafiya, ya baka tsawon rai ya bamu nasarar ɗaukar fansar abun da aka yi mana. Har cikin raina nake jin zafin abun da ya faru da kai, but before then. Please promise me ka daina z1y ³y2ubar da hawayenka, wanda ka yi ya isa. Kuma kayi mini alƙawarin ba zaka sake shan ƙwayoyin da za su illata mini kai ba" Liti ya tashi ya ce "Nikam nayi waje, wannan wace irin fitsara ce?" "Ka kalleni mana dan Allah" ya ɗaga kansa ya kalleta. Duk da idanunsa sun yi mata nauyi, amma ta ce "Ka ce Nabila, nayi miki alƙawari ba zan sake shan miyagun ƙwayoyi ba, ba zan sake yi wa kaina allura ba, zan baki cikakken goyon baya in ɗauki fansata ta hanyar da ta dace" "Tashi zan kwanta" ya faɗa a taƙaice. Duk wannan zubar da ta gama yi, ba su ne a gabansa ba, kawai ta tashi zai kwanta. Ta fuskanci aiki ne jawur a gabanta, ba ta sare ba taƙi tashi, ta kuma ƙi magana. Ya ture ta, ya raɓa ya kwanta ya juya mata baya. "Allah ya baka lafiya ya jaddada rahamarsa ga marigayyiya jauhar". "Amin ya Allah, na gode" yayi maganar idanunsa a lumshe. Tayi murmushi jin ya amsa, ba ya wasa da duk abun da ya shafi Jauhar. Walid ne ya rakota, take ce masa "Ku yi haƙuri da wasu abubuwan da zaku ga ina yi, ina yi ne saboda sama wa ƙwaƙwalwarsa nutsuwa, idan ba haka ba zai iya rasa hankalinsa baki ɗaya" Walid ya ce "Karki damu na fahimce ki, ki rabu da liti, ba kan gado ya cika ba dama". *** Ramma na kwance a jikin Abdul, yana waya da mahaifiyarsa, tana yi masa magana a kan haɗa lefensa, ya ce su yi duk abun da yakamata, yau zai je asibiti ne, zai yi tiyata cikin dare, dan haka yayi busy. Ya kashe wayar, ramma ta motsa tana ƙoƙarin tashi ya riƙe ta ya ce "Beb, ina zaki kuma?" Rai a haɗe ta ce "Na gaji da kwanciyar tashi zan yi" Ya tashi zaune ya ce "Haba rahama, nifa duk wani motsinki ina gane me kike nufi, ai na baki haƙuri, kin san dalilin auren nan..... "Ni cewa nayi na damu da aurenka? Ina ruwana ne ni damuwata na koma gaban iyayena" Abdul ya ce "Zaki koma, amma sai Allah ya sa kin samu ciki kin haihu, am doing this for your own benefits, saboda ke duk nake haka". "To bana so, ka daina" "Haba sayyada, ba fa zina zan yi ba aure zan yi, kin ce in yawaita istigfari Allah zai yafe mini, to ke kuma kin ƙi ki yafe mini, ki yi amfani da iliminki mana haba sayyada rahama" "Ba wata sayyada, sayaddar da ka kafawa ƙahon zuƙa sai ta haifi ɗan shege ko?" Kawai ya kama dariya, ya ce "Ke dai ba a iya miki, idan an yi nan sai ki yi can, anjima zan kai ki shan ice cream mu ɗan fita mu zagaya". "Ba zan je ba" Ya ce "Shikenan huta roro, na ɗauki amaryata mu je" Tayi tsaki, ta sauka daga kan gadon, ta nufi toilet. ***Bunkure ta fito daga shari'a kenan, ta nufi motarta, ta tarar da Nabila a tsaye tana jiran isowarta. Ta tsaya ta kalli Nabila, Nabila ta kalleta ta ce "Na je office ɗin ki sau biyu, an ce ba kya nan, kin yi balaguro, da ki ka dawo kuma, bani da isashshen lokaci. Ina son sanin in da ramma take, ita wadda aka yi wa fyaɗen, da shi kansa likitan da yayi documenting ya tabattar da an yi mata rape, ba wai takarda kawai ba. "Ke, kin fara wuce gona da iri fa, kar ki bari na waiwayeki, nayi yinƙurin ɗaukar mataki a kanki" "Wane matakin kenan? Harka ce ta aiki fa, idan kina da gaskiya menene na ɓoye-ɓoye. Nayi mamakin yadda kina mace, once a rape victim, amma ki zama tsanin kare masu laifi. Na san kin ga shaidar da na gabatar a kotu, ta sautin muryar mahaifiyar ramma, kuma ko sama ko ƙasa an nemeta an rasata yanzu. Shikenan idan kina taƙama da kun saye lawyoyi da alƙalai, ki shirya motsi na gaba da zan yi. Sai na bankaɗo duk wani shu'umanci, da zalunci da ki ke yi, kuma ko a ina kuka ɓoye ramma, sai na tona muku asiri, na tonawa wanda yayi mata fyaɗe asiri. Kar ki manta ɗan hakin da ka raina....... Bata sake cewa komai ba ta tafi ta bata wuri. Wayarta ta ɗaukko ta tura wa Indabo message. "Yakamata ka motsa a kan yarinyar nan, ta fara wuce gona da iri" Kasancewar ta sha zirga-zirga, a gajiye ta ƙarasa office ɗin su. Wurin Barrister Habib ta fara nufa, tana zuwa ta tarar da Sumayya da wasu mata su biyu, a Office ɗin Barrister Habib suna jiranta. Suka gaisa da Habib, ta juya ta fice, zai yi magana, Sumayya ta ce "Bari na je na same ta. Ta iske Nabila a office ɗin ta, ta ce "Arfa, tun safe fa bayin Allah nan suna jiranki, har na zo nima, baki zo ba ina ki ka je ne haka?". "Sumayya wai baki da zuciya ne, alaƙa da ke ce bana so, na menene zaki din ga bibiyata kuma?" "Nabila, dan Allah ki tsaya mu yi magana, mu fuskanci juna dan Allah" "Babu wani abu da zan fuskanta, ni kin riga kin sire mini, ki fita ki bani wuri, ko ni baki wuri" Sumayya ta tsaya tana kallon Nabila. Nabila ta zo zata fice, Sumayya ta riƙe ta, ta ce "Ni yakamata na fice na baki wuri, na san nayi kuskure amma yakamata ace ko sau ɗaya kin saurare ni. Tabbas ina bayar da duk wasu bayanai, da aka nema a kanki, amma ni baki san a wani hatsarin rayuwata take ciki ba, domin kare taki. Ni 'yar halak ce, zan daina binki dan ki saurare ni, amma zan cigaba da aikin da aka bani a kanki. Idan kin ga dama, ki saurari matan can, idan kuma kin ga dama, ki kore su, matsalarki ce ba tawa ba" ta ja da baya, ta buɗe ƙofa ta fita. Ta so bin bayan sumayya, amma sai ta fasa, Sumayya ta faɗi maganganu masu muhimmanci, da yakamata ta tsaya ta ji menene, amma sumayya ba ta fushi, idan kuma tayi tana da wahalar sha'ani, dan haka bata bi bayanta ba ta koma wurin barrister Habib da wannan matan. *** Ƙarfe biyar Al'amin ya koma maɓoyarsu, bayan su Walid suna ta fama da shi, ya ce a sallame shi, sun ce sai ya gama warwarewa, shi kuma ya san akwai hatsari zamansa a asibitin, suna fita salla ya fice daga ɗakin, ya bar Asibitin. Sai dai yana shiga ɗakinsa, ya tarar da wata baƙar rigar, irin wadda aka ajiye masa da safe a asibiti, ya ɗaga ta ya juya, irin waccan ce sak. Ita ma a take ya yayyagata, ya watsar, ringing ɗin waya ya ji a ɗakin, ya duba ya ga wata ƙaramar waya keypad, wata lamba ce ke kiran wayar. Ya ɗaga ya saka a kunnensa. "Al'amin Viper, ka daina jayayya da ƙaddararka, bin wannan ƙaddarar itakaɗaice mafitar da ta rage maka, ka karɓi kayan da muka baka, ka dawo gida Viper" aka katse kiran, ya bi lambar, amma aka ce lambar dose not exist. Yayi jifa da wayar ya ja da baya ya tsaya yana huci. Ayshercool 08081012143 60 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Ya cigaba da zazzare ido, yana kallon ɗakin, ya ɗauki wayar da ya watsar, ya sake haɗata, ya kuma kiran lambar, amma a sai ace masa lambar dose not exist. Ya fita waje, ya zagaye gidan yana dube-dube amma bai ga kowa ba, ya koma cikin gidan ya ɗauki wayar da rigar da ya yayyaga, ya shiga banɗaki, ya watsa su a masai ya fito. *** Nabila kuwa bayan tafiyar sumayya, ofishin Barrister Habib ta koma, suka sake gaisawa da matan nan, ya ce "Ina sumayyan?" "Ta tafi gida ne, na ce gani me yake tafe da su ne?" Ya kalle su sannan ya kalli Nabila ya ce, maganarki da ki ka yi, su sumayya T ladan suka saka a radio, a kan Barrister Naja'atu Bunkure, shi ne ya sanya suka zo, su sanar miki da wasu abubuwa da zai taimaka miki". Nabila ta ce "Masha Allah, bari na aika baba masinja, ya sayo musu ruwa da lemo, naga azahar ta wuce, kafin nan nima nayi salla" Ya ce "To babu laifi" Tayi salla ta dawo, suka zauna da matan, ɗayat ta fara bata labarin abun da ya faru "Ni 'ya ce da ni, mun rabu da mahaifinta, tana wurin babanta, yayi mata auren dole, take ta guje-guje saboda ba ta san mijin. Ake ta fama har tayi yinƙurin kashe kanta, magana har gidajen rediyo, ta turo wakilanta, suka tafi da mu can office ɗin ta, ta ce aure ba dole bane ba, dan haka dole a kashe auren nan. Da fari na so ayi sulhu yarinya ta koma ɗakinta, tun da bama tare da ubanta. Na din ga yi mata nasiha, a kan tayi haƙuri, tun da babanta yana ta tsine-tsine a kan ta bujire masa, ta haƙura ta yarda, amma matar nan ta ce sai an kashe auren, zata kai ni ƙara hukumar kare hakkin ɗan Adam, ta ɗauke mini 'ya, ta tafi da ita, sai da aka yi sati biyu sannan ta dawo mini da ita ga babanta da mijinta suka ƙara matsa mini lamba, bayan ta dawo da ita, yarinya ta ƙara tuburewa ba ta san zancen aure ba. Tamkar an canza mini ita, idonta ya buɗe, har mijin 'yar tawa ta saka aka kama aka rufe, aka kashe auren nan. Yanzu maganar da nake yi miki, shekru uku kenan, yarinyar nan ta ce aure wani abu ne al'ada da muke takurawa kanmu a kai, addini bai wajabta mana ba, haka take rayuwarta, sai ta shafe kwanaki ba ta gida, tana yawonta. Babanta ya sallama mini ita, bayan ya gama tsine mana daga ni har ita. Har a cikin unguwa ta cigaba da yi wa sauran ƙasayenta mummunar huɗubar adawa da aure, wai ana tauye musu hakki, kuma wallahi Naja bunkure ce ta mayar mini da 'ya haka,tana fakewa ne kawai da taimako, tana zaluntar mutane". Ɗayar ta ce "Nima kusan hakan ne, wani yaro ɗan masu kuɗi, ya lalata mini yarinya daga aikenta gidan, jami'an tsaro suka ƙi kama yaron, uban ɗan ya ce in dai arziki yana rana, zai kare ɗan sa, ba wanda ya isa ya kama shi ya hukunta. ni kuma jin shirye-shirye da ake yi a kanta, na taimakon marasa galihu, ya sanya nima na je neman ta taimaka mini. Da farko abu kamar gaske zata taimaka mini, ƙarshe abun ya juye, aka nemi a mayar da case ɗin wai sharri muka yi wa yaron. Wallahi ƙarshe yarinyata fiya-fiya ta sha ban sani ba, yar shekara goma sha huɗu ta mutu. Wallahi matar nan azzaluma ce, bamu da wurin da zamu je, mu nemi hakkinmu sai wurin Allah, haryanzu idan zance yayi zance a kan tayar da maganar abun da ya faru da yarinyata, wanda hakan ba ƙaramin tsaye mini yake yi ba" tayi maganar tana kuka mai ban tausayi. Nabila ta tashi ta rungume matar, tana rarrashinta ta ce "Ki yi haƙuri dan Allah, ki kwantar da hankalinki, Allah ya jiƙanta, kuma in sha Allah da ikon Allah sai mun kai matar nan ƙasa, zan yi iya yi na, in bankaɗo duk wani mugun abu da ta aikata muku, kuma sai ta girbi abun da ta shuka, ku yi haƙuri. Yanzu duk zaku bani adress ɗin ku, zan bi cases ɗin ɗaya bayan ɗaya, na tabattar da abun da ya faru kafin na san abun yi" Jikin Nabila yayi sanyi sosai da sosai, da jin abubuwan da Bunkure take aikatawa, tamkar ba 'ya mace musulma ba, da matan ke iƙrarin ciwon ƴa mace, na 'ya mace ne. Har kuɗin mota ta basu, bayan tafiyarsu ta kalli barrister Habib ta ce "Yaya habib, ka ji wani yahudanci? Ina laifin ta tsaya a kan iya kashe auren an yi wa 'yar auren dole?" "Ke ce baki san wacece ita ba sai yanzu, wannan wata ɓoyayyiyar aƙidarta ce, na bawa mata damar ƙin zaman aure da lasisin karuwanci. Tana saye yaran da kuɗi, da abun duniya wurin cusa musu wannan mummunan ra'ayin, da koyar da su daidaiton jinsi tsakanin su da maza". "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, amma duk da haka Alhamdilillah, na samu hints a kan yadda zan bankaɗo asirin matar nan, and one more thing kuma" ya kalleta ya na jiran me zata ce. "Maganar da muka yi da kai kwanakin baya, a kan case ɗin Aminu Viper" "Ina jinki" "Naja'atu Bunkure tana cikin tawagar lauyoyin da suka tsaya kai da fata a kan shari'ar da aka yi masa. Kuma ka san ita ungulu ce ba ta jewar banza, dan haka akwai manufa a cikin shiga shari'ar da tayi. Viper ba ɗan siyasa bane ba, kuma ba shahararren mai kuɗi bane ba, balle ace tsaya masa tayi a shari'ar. Dan haka akwai ayar tambaya a kan charges ɗin da aka yi masa na kisan kai. Take a look at it barrister, an tsare mutum shekara biyar, an yi masa shari'a sau biyar kawai, an kai shi prison an ajiye babu conclusion na shari'ar, is je guilty or innocent? Kwatsam an ce ba a ganshi a prison ba, kuma an cigaba da nemansa, ruwa a jallo, anya akwai gaskiya a lamarin nan kuwa?" Ya tsura mata har ta gama, yayi murmushi ya ce "Haka kwanyar nan take cike da basira, amma aka ƙarar da ita a wurin iyayi da kwalliya?. Maganarki gaskiya ce Nabila,  amma ina rabaki da case ɗin Vipern nan, akwai badaƙala sosai a kan case ɗin". Nabila ta ce "Me da me ka sani a kai?" "Nothing much, kawai na san dai akwai bita da ƙulli ne a ciki sosai" Ta jinjina kai ta ce "Haka ne, bari na tafi gida, yau a matuƙar gajiye nake" tayi masa sallama, ta tafi office ta ƙarasa shirinta, ta tafi gida. Ta sake karo da file a office ɗin. Cikin mamaki ta ɗauka, ta fara buɗewa. Aka rubuta continuation a ciki. Cigaban tarihin Naja bunkure ne, bayan rape da aka yi mata, cousin brother ɗin ta, aka rufe case aka ce abu ne na dangi, bayan ta ƙara girma tayi aure, ta sha wahala sosai a hannun mijinta na farko, ya azabtar da ita tamkar baiwarsa, ko haihuwa ba ta yi ba auren ya mutu. Yayanta ne ya taimaka mata, ya mayar da ita makaranta, tayi candy, ta shiga jami'a, sai dai bayan rasuwar yayanta, aka rasa mai sponsiring ɗin ta, ta cigaba. Mahaifiyata na can wani garin tana aure, babanta kuma ya ce ba ruwansa da ita, tun da taƙi zaman aure. A lokacin har wurin ɗan majalisar su, ta je neman kuɗin makaranta, lokacin yana tare da Indabo, indabo ya ce zai bata, amma sai dai ayi bani gishiri na baka manda. Ta amince tun daga nan, ta zama tamkar matarsa su watse ya biya mata kuɗin makaranta, babu wani sirri nasa da bata sani ba. Ta nemi ya aureta, bayan tayi graduation, amma yaƙi, ganin haka ya sanya, ta samu wani suka daidaita ya aureta, sai dai Indabo ya cigaba da bibiyarta. Ta fara aiki a matsayin lawyer mai zaman kanta, Naja tana da burin yin luxry life sosai, sai dai mijinta yana da rufin asiri amma ba irin wanda take hange ba, Indabo yayi mata alƙawarin haɗa ta da manyan mutane, lokacin ya zama ɗan majalisa, wanda zata din ga samun alkhairi da damarmaki. Kwaɗayi da buri, ya sanya suka koma ruwa da aurenta, ya din ga kashe mata kuɗi, yana kuma haɗata da manya. A wurinsa ta koyi shaye-shaye. Tsakanin ta da mijinta babu ragayya ko kyautatawa, duk son da yake nuna mata da kulawar da yake bata sam baya gabanta. Ta fara tashe sosai tana shahara, ana programs da ita a kafafen watsa labarai, ta buɗe ƙungiyar ta ta kanta, bayan joining ɗin ƙungiyoyin yahudawa, masu da'awar daidata jinsi, reshen Nigeria, ta cigaba da yi musu aiki ta ƙarƙashin ƙungiyar ta. Sai dai a haka take miyagun harƙallarta, na yi wa manyan mutane safarar mata a birnin tarayya, musamman ƙananan yara, da akan yi amfani da su saboda asiri. Red handed mijinta ya kamata, chats ɗin ta da wani minista, na ƙazanta, yayi kuka, amma ko a jikinta, ta ce idan ba zai iya ba ya rabu da ita. Haka ya saketa, ta samu cikakken gashin kanta. Ba ta taɓuwa, ko da kuwa tayi laifi, yanzun nan ƙungiyoyin kare hakkin ɗan Adam zasu shiga lamarinta. Ta din ga binne mutane ta hanyar bayyana musu kyawawan ayyukanta, da ɓoye na laifin. Bayan mutuwar aurenta labari ya bazu, mutane suka din ga tsinewa mijinta, wai ya saki macen kirki, aka yi hira da ita, ta din ga kuka tana yi tsohon mijinta sharri kala-kala. End the story.... Aka rubuta a ƙarshen page ɗin. Wani irin gumi, ya din ga tsatstsafowa Nabila, ta ma rasa abun yi, da tunanin da yakamata tayi, ba ta bari ta takura ƙwaƙwalwarta wurin hasaso waye ya kawo mata file ɗin a karo na biyu ba, kawai ta ɗauki jakarta ta fita. *** Sumayya ce a tsaye tana kuka wiwi, shi kuma ya zuba mata ido, ko ƙiftawa baya yi, sai da tayi mai isarta sannan ya ce "Kukan ya isa haka, meyafaru?" Ta share hawayenta ta ce "A gaskiya sir, ni na gaji da aikin nan, na samu matsala da ni da Nabila, ni Nabila ba ƙawata ce kawai ba, ƴar uwata ce, ta riga ta yi fushi, ba zata saurare ni ba, ni ban san wanda ya gaya mata ina bibiyarta ba, ga wancan honorable ɗin ya addaba mini, duk motsina sun sani, sai kuma sun tambaye ni, me tayi me take ciki, banda barazana da suke yi mini ba yau ba gobe, ni dai dan girman Allah ka yi wani abu a kai, kar ni ko ita ayi wa wani illa, indabon nan fa ba imani ne da shi ba" ta ƙarasa maganar tana sake fashewa da kuka. Yayi murmushi ya ce "Haba ƴar jarida, ya da kuka wiwi haka da karaya nan da nan? Da kin sanni, kin san zan taimake ki? Baki san ya aka yi na gane Indabo yana yi miki barazana ba. Har na shigo lamarin ba, dan haka ba zan bari a cutar da ku ba, dukkaninku a kan gaskiya ku ke, sai dai ita naga buyaginta yayi yawa. Ki yi haƙuri ku daidaita, da haka zan cigaba da yi mata supplying abubuwan da take buƙata a harkar shari'ar nan" "Sir yanzu fa ka gama cewa buyaginta yayi yawa, sai ce mini munafuka take yi, babu yadda tsakanunmu yanzu" Ya ce "No, tayi fushi ne kawai, and ki ƙara kiyayewa sosai da sosai, ki daina bari tana gane kina bibiyarta". Sumayya ta ce "Yanzun ma, wallahi ina kiyayewa, ban san yadda aka yi ba" Ya din ga rarrashinta, sannan ya saka aka ɗauke ta a mota, aka mayar da ita gida. *** Nabila da ƙyar ta isa gida, ta watsar da kayan a kan gadonta, ta fara kiran wayar Viper, amma a kashe, ta kira ta Walid amma baya ɗagawa, haka ta haƙura ta shiga banɗaki tayi wanka ta yi alwala ta fito. Har washegari da safe, Nabila tana neman layin Walid, hankalinta ya ƙara tashi, tayi tunanin ko wani abun ne ya same shi. Tana saka kayan abinci a motarta, Nasir ya fito. Ta ce "Yaya ina kwana?" Ya amsa da "Lafiya ƙalau, wai ina ki ke zuwa da kwanukan abinci kwana biyun nan ne?" Ta ɗago ta kalleshi ta ce "Ci nake yi mana, wataran ai wuni nake yi bana gida" Ya ɗage kafaɗa ya ce "Ban sanki da dakon flask ba, saboda haka kin gwammace ki ci biscuit da sauran kayan ciye-ciye" "Haba yaya, yanzu ba mota ce da ni ba? Kuma zan je in ta cin abinci nikaɗai duk ga mutane ne a wuri?" Ya girgiza kai ya ce "A'a, amma yanzu ƙarfe bakwai saura kwata, har shida da rabi kin fita, saɓanin da har goma saura sai ki kai a gida" Ta tsaya sosai ta dube shi ta ce "Yaya me kake nufi ne? Ka daina ɓoye-ɓoye ka fito fili ka sanar mini cewar, tuhumata kake yi, da aikata rashin gaskiya mana" Yayi murmushi ya ce "Ai ba a tuhuma sai an tabattar da zargi my dear" "Da ka daina zargin, dan wahalar da kanka kawai zaka yi, ko kuma irin abun naku zaka yi mini na masu kaki" tayi maganar tana murmushi. Shi ma murmushin ya yi, ya ce "A sauka lafiya" Ta amsa da Amin ta tafi. Tana tafe a hanya sai ga kiran wayar Walid, ta ɗaga wayar ta ce "Oga Walid, sai kiranka nake yi a waya, shi wayarsa ba ta shiga, wayarka kuma baka ɗagawa" Walid ya ce "Bari kawai, kin san halin mutumin naki sai a hankali ai, jiya bayan tafiyarki, ya kafa mitar sai an sallame shi daga Asibiti, da mu da likita muka din ga rarrashin sa, yayi mana banza, mun fita salla ya gudu, baki ga yadda hankalinmu ya tashi ba, na ce musu kawai mu koma gida, dama ya saba irin haka, ko lokacin da ƙanwata take raye, haka take fama da shi, idan aka kwantar da shi, da ɗanyen ciwo haka zai bar asibiti sai dai ta ƙarasa masa dressing a gida ya warke". Nabila ta ce "Allah sarki, Allah ya yi mata rahama, shi kuma ya bashi juriya. Kana ji na, zan shigo dan ga abinci ma nayi, yayana ya fara saka mini ido ne, dole na canza takuna, zuwa azahar zan bar motata a chamber, zan zo in sha Allah" Ya ce "To Allah ya kawo ki, dan zuwan naki yana da amfani, yaƙi cin abinci ya ƙi shan magani, yana kwance kawai tun jiya" "In sha Allah zan zo, ayi masa sannu" ta ajiye wayar tana murmushi, rigimar Viper tana da yawa, idan ba ka da haƙuri ba zaka iya da shi ba. Har ta fara neman lambar sumayya, sai kuma ta fasa kiranta, dan har ta manta sun yi faɗa. Kawai ta din ga jin ta wani iri, akwai abubuwa da dama da take son gaya wa sumayya, saboda kusancinsu da shaƙuwarsu, ta musamman ce. Sai dai haryanzu tana mamakin dalilin da zai sanya a din ga bibiyarta ta hanyar sumayya, kuma waye yake bibiyar ta ta. Sai dai ta fara zuwa courts ɗin da take da trials, ta gabatar da shari'oi, sannan ta koma asibitin da aka kai ramma, lokacin da aka yi mata fyaɗe. Ta nemi a bata copyn report ɗin da aka yi confirming rape case ɗin, aka ce an bawa ƴan sanda. Ta nemi ganin likitan da ya kula da ita, aka ce ya tafi ƙaro karatu, a bata lambarsa nan ma aka cigaba da yi mata yawo da hankali. Sai da ta gama zagayenta, sannan ta ajiye motar a wani wurin parking, ta karɓi pass, ta tafi wurin su Viper. Yau a tsakar gida ta tarar da shi, sun shimfiɗa masa tabarma, yana zaune yana ya danna wayarsa, sai dai idanunsa sun ɗan yi wuri wuri ya faɗa, gabansa kuma kwalin sigari ne da lighter. Tayi sallama duk suka amsa, ya ɗaga kai ya kalleta ya mayar ya sunkuya. "Ohhh masha Allah, the most handsome man ever saw, kaga yadda ka yi kyau sosai da sosai" ta nemi wuri ta zauna a gabansa ta ce "Manya gatan wasa, fisabilillahi mutum sai ya gudu daga Asibiti ba a sallame shi ba? Idan kuma bai warke ba fa, ni gaskiya ban ji daɗi ba" Ba ta saka ran zai kulata ba, ta ce "Ina wuninku, ya mai jiki kuma?" Suka amsa da sauƙi. Walid ya ce "Ba yadda bamu yi da shi ba, amma sai nemansa muka yi muka rasa" Tayi dariya ta ce "My, ya kake haka ne, duk muna ta taka, amma kai ko a jikinka. Wannan sigarin ina fatan ba sha aka yi ba, kaga an ce jininka ya hau, kuma kana smoking ba zai sauka da wuri ba, an ce mini baka cin abinci, duk ka rame ai ba zan ji daɗi ba" ta janyo ledar abinci ta ce "Ka yi haƙuri ban kawo abinci da wuri ba, Yaya Nasir ya fara saka mini ido" ta ƙarasa maganar tana miƙa masa plate, da cup ɗin da ta zuba masa kunun alkama. Ya saka hannu ya karɓa, ya fara ci. Liti ya ce "Wato mai zamani mune dai ba ma yi maka gwaninta ko?" Nabila ta yi murmushi ta ce "Ka san wani abu?" Ya girgiza mata kai alamar a'a. "Ni fa na gaya wa Sumayya, na san tana bibiyata, duk da jiya ta kawo mini wasu mata, da suka yi mini complain a kan Bunkure, amma mun yi faɗa da sumayya. Sannan an sake ajiye mini file a office ɗina, na ƙarashen labarin Naja'atu Bunkure. "Ku ka yi faɗa ba ƙawarki ba ce ba?" "Eh, amma meyasa zata ci amanata?" Ya kalleta ya ce "Ya aka yi ki ka tabattar da cin amana ne ya sanya take bibiyarki?" "Saboda kai ka gaya mini" "Ban ce tana bibiyarki dan ta ci amanarki ba, kuma baki da tabbacin da gaske nake ko akasin haka" Ta gyara zamanta ta ce "A labarinka da na ji, baka ƙarya dan ka ci amana, kuma bana tunanin zaka fara a kaina" Ya jinjina kai ya ce "Bani wayarki" ta ɗaukko wayarta ta bashi, ya nutsu sosai yana ta daddanawa. "Yayanki ma na ƙoƙarin yi wa layinki kutse, sai dai na rufe damar hakan. Yana zarginki a kan da shi kansa bai san menene ba. Yayanki ya ga Indabo yana yi masa aiki a kaina, yana kuma gargaɗin sa a kan abun da ki ke yi a kan bunkure, na san zuwa yanzu ya matsa miki lamba a kan ki rabu da ita" Ta waro ido ta ce "Ya aka yi ka sani? Anya yayan kuwa?" Ina bibiyar kiran wayarsa ta hanyar amfani da wayarki, hakazalika duk wasu maganganu da yake yi, recording ɗin suna kan computer ki. Wayarsa da Indabo kawai nake bibiya, ba ruwana da sauran harkokin sa. Ta ce "Subhanallah, amma yaya ya bani kunya, shiyasa yake ta uzzura mini? Amma nima ka yi hacking ɗin wayata kenan? Kana jin duk wayar da nake yi da samarina?" Tsaki yayi, ya jefa mata wayarta. Ya ce "Ina magana serious kina yi mini shirme?" Ta ce "To ai kar ka ji ina kalamai ne, ka zo kana kishi, nifa duk ba son su nake yi ba, kai kawai nake so" tayi maganar da niyyar sake kunna shi. Ƙoƙarin tashi yayi, tana dariya ta ce "Yi haƙuri, dan Allah ka duba mini ƙarashen labarin nan, na Najar bunkure ka gaya mini menene opinion ɗinka". "Mu yi aiki kawai, ki daina yi mini wannan shirmen" "Ba shirme bane ba fa, ni da gaske nake" ya karɓi file ɗin, ya cigaba da duddubawa. Ya ɗaga kai ya kalli walid ya ce "Mai laya" "Mai zamani". "Yakamata ku je ku daba mini mahaifiyar Nura, tun da na fito yakamata ace na je na ganta, amma ba zan iya ba, ban san wace irin karɓa zata yi mini ba, maybe ita ma irin kallon da ake yi mini, take min" Liti ya ce "Haba maza, babu lallai gaskiya" Nabila ta ce "Ina kakarka to? Wadda oga walid ya bani labarinta?" "Ta mutu ina prison" Walid ya ce "Har tare da ita mun je prison, sau biyu ba a bari mu ganshi. Baiwar Allah nan tashin hankali da damuwa ne, suka haɗu suka kasheta" Jiki a sanyaye ta ce "Allah sarki, Allah ya yi mata rahama, ya sanya sun huta baki ɗaya, da yar madara, da Hajiya, da mamana da sauran al'ummar musulmi baki ɗaya" suka amsa da Amin. Walid ya ce "Mamanki ta rasu?" Ta jinjina masa kai ta ce "Eh, ban ma santa ba, sai dai hotunanta na gani a wurin Abba" "Allah sarki, Allah ya jiƙanta" Liti ya ce "Shiyasa ba kya ji, ina tausayawa mariƙanki, sun sha wahala da ma ba kowane maraya ne yake ji ba" "Oganku shi ne na farko a marasa jin, in dai maraya baya ji" ta yi maganar tana satar kallon Viper. "Amma Viper, ka sake komawa wurin Abbanka kuwa? Na san zuwa yanzu ya huce, zai kuma fuskance ka, ka yi masa bayani, shi fa tsakanin ɗa da iyaye sai Allah" yayi mata shiru. "Ni ka bani dama naje na same shi, na san zai fahimce ni" Ya ajiye file ɗin ya ce"Kar ki kuskura ki fara wannan gangancin, kar ki kusanci unguwarmu, ko ki ce zaki je unguwar da gidana yake, idan ki ka yi ɗaya daga ciki, zan yanke aikin da zan yi da ke, kuma hakan zai iya sanya wa  na kashe ki" "Au ba zaka daina zancen kisan kan nan ba ko? To maza nima ka kashe ni, na ga wanda zai din ga rarrashinka. Ta tashi ta ɗauki jakarta, ta tattara kwanukanta, ta ce "Bari na tafi, kar nayi yamma da yawa, zamu yi magana" tashi ya yi ya ce "Muje" "Rakani zaka yi? To muje" suka fita kamar gaske. "Ina sake gargaɗinki, kar ki sake ki ce zaki nemi gidanmu ki je, ko gidan su 'yar madara, zaki ɓata mini aiki, duk da na samu labarin sun bar unguwar, idan kuma ki ka ɓata mini aiki, ba na jin zan iya yafe miki" Ta ce "Subhanallah, in sha Allah ba zan je ba, amma yakamata ku daidaita da mahaifinka. "Ba wannan ne a gabana ba" "To menene a gabanka? Iyaye fa ba a fushi da su" "Ki rabu da ni" Ta ce "To, Allah ya baka haƙuri" "Ki cigaba da kula sosai da sosai a kan zuwanki wurin nan, za a iya biyoki har nan, bana tunanin iya wayarki ake bibiya" Ta kalleshi ta ce "Akwai wata mota da na lura da tana bina kwanakin baya, amma ba wannan ba. Na faa tunanin anya a cikin yaranka babu wanda suke sanar da wasu abubuwan da muke yi? Ko kuma wani yana binka ko kuma ni da ake bi, an san ina zuwa wurinka ba? Suwaye suka ɗaukeka kwana biyu? Sannan ya aka yi aka san kana asibitin nan, har aka biya maka kuɗin asibiti" Ya sauke numfashi ya ce "Kar ki shagala da tunani da yawa, ki manta da abubuwa masu muhimmanci, ki je zamu yi magana" Ta kalleshi ta ce "To, amma dan Allah ka ɗaga wayata da daddare in ji muryarka, ka ji Oga" wani irin mugun kallo yayi mata, ya nausa ya bi wata hanyar, ita kuma tayi gaba tana murmushi. *** Ramma na zaune a kusa da Abdul, yana kallon ball, ita kuma ta kunna radio a wayarta, tana ji. Ya kalleta ya ce "Dan Allah ki rage radion nan" "Ina ruwanka da ni ne, ka yi kallonka mana" "Kin cika mini kunne da radio ne" "To ita ball ɗin magana ake yi? Ba ihu bane ba kawai?" Abdul ya ƙure volume, ita ma ta ƙure volume, ta kara masa radion a kunnensa. Yayi mata shiru ya ce "Kya yi kya gama" Sumayya ce tare da murtala a studio, suka gabatar da program, kasancewar an samu akasi masu gabatar da program a dai-dai lokacin ba su samu zuwa ba. Program suke yi akan abubuwan da suka shafi rayuwa, suna yi suna karanto saƙonnin masu sauraro. Murtala ya ce "T ladan, ga wata tambaya daga masu sauraro, wai an ce a tambayeki, wace irin alaƙa ce tsakanin ki da Nabila Yusuf maitama, da kullum ba kya taɓa aiki ki tashi, baki ambace ta ba, baki tsokane ta, ko saka waƙoƙi domin jin daɗinta ba?" Sumayya ta yi murmushi ta ce "Barrister Nabila, voice of voiceless a lady of her words, a hardworking, strong minded young barrister, she's exceptional, lovely and simple sister of me" tayi maganar tana jin zafin saɓanin da suka samu a tsakanin su. Murtala ya ce "Tirƙashi, duk wannan kirarin itakaɗai?" "Sosai, Nabila mutum ce ta mussaman a rayuwata, ina yi mata son fisabilillahi" "To yanzu da saurayinki, da Nabila wa ki ka fi so?" Ta kwashe da dariya ta ce "Uncle murtala wannan ai haɗa faɗa ne" "To yanzu kafin muyi sallama da masu sauraro, gaya mana kalma ɗaya tak a kan Barrister Nabila" "Mai gaskiya ce, ina yi mata fatan nasara, ya ɗaukaka mini ita, ya kuma kare mini ita a duk in da take, ya dauwwamar da ita a kan gaskiya" Murtala ya ce "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum, Allah ya bar wannan ƙauna, kafin mu ƙarƙare shirin, mun karɓi takardar wata baiwar Allah da za a yi wa ɗanta aikin ƙaba, amma ba ta da hali, tana neman taimakon bayin Allah. Akwai kuma wadda take neman kuɗin sayawa mahaifiyarsu magani mai fama da hawan jini, muna fatan zaku taimaka" Nabila kuwa tana driving, ba ma'abociyar jin radiyo bace ba, amma saboda sumayya take sauraren radio. Hawaye ta din ga sharewa, tare da tuna abun da ta yi wa sumayyan. Ramma kuwa cewa ta yi "Allah ya ƙarfafi wannan baiwar Allah, ya tabattar da ita a gaskiya, kar ya kauce hanya, kamar waccan munafukar mara imani" Abdul yana jin ta, yayi mata shiru. Ganin bai kulata ba ya sa ta ce "Ba zaka ce amin ba" "Ni fa ball nake kallo" "Allah ya sa a cinye club ɗin da kake yi" "Ba amin ba" ya ɗauki wayarsa, ya kira admin ɗin asibitin sa, ya ce a je gidan radion su sumayya, a kai yaron nan ayi masa aiki kyauta, mai hawan jinin ma a kai ta a bata magani. Ramma ta ce "Kalle shi kamar na Allah" duk yaƙi kulata, ta tashi ta nufi ɗaki, ta saka hannu ta kashe tv ta riga ɗaki da gudu, kawai yayi dariya. *** Kwanaki biyu, Nabila ta daina samun Viper a waya, sai dai da ta kira walid, ya tabattar mata da lafiyarsa ƙalau. Nabila ta fara gazgata zancen Viper, duba da yadda Nasir yake kashe-kashen kuɗi, ya canza mota ya cigaba da gininsa, kuma salarynsa gaba ɗaya ba wani shahararre bane ba. Nabila tana kwance tana waya da Alhaji Wada M karofi, yadda yake lallaɓata yake yi mata magana, har kunya yake bata. Fuskar viper kawai take hangowa, yanzu da shi take yi wa kalaman nan, da tuni ya haɗe rai yana hararta. Bayan sun yi sallama ta ajiye wayar, Walid ta shigo ɗakin ta ce "Arfa, isa ne ya shigo yanzu, wai ana sallama da ke a waje" "Kai, wane ɗan baƙin cikin ne zai hana mini jin daɗi a magaribar nan? Ni fa ban yi da kowa za a zo wurina ba" Walida ta ce "Ace ya tafi kenan?" "A'a gani nan zuwa" Ta yafa mayafin abayarta, ta fita, a ƙa'idar Abba a cikin gida suke zance, ganin bai shigo ba, ya sanya ta gane lallai wanda ya zo ɗin baƙo ne. Ta zira kai ta leƙa ƙofar gida, dan duba waye. A opposite ɗin gidan ta ga Viper a tsaye yana kallon ta. Ayshercool 08081012143 61 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Gaban Nabila ya faɗi, cikin matsanancin tsoro da tashin hankali, ta din ga waige-waige tare da dubawa, idan akwai wanda ya ganshi, amma layin babu kowa, sai manyan security light da suka haska ko ina. Ta sake kallonshi, ta tabattar shi ne, ta ƙarasa in da yake da sauri ta ce "Viper, waye ya nuna maka gidanmu? Yau kuma ba office ba har gida?" "Akwai matsala ne?" Yayi maganar yana ƙara ƙureta da ido. "Au tambayata ma ka ke yi? Amma dai ka san yayana nemanka yake yi ko meyasa zaka zo gidanmu, lallai sai ka tona mini asiri ne? Waye ma ya nuna maka gidanmu?" "Shi yayan naki, ki shiga ki gaya masa gani ya zo ya kamani mana, shikenan ki daina wahalar da kanki da fargaba mana. Kina tunanin zan yi aiki da wadda ban san wacece ba?" Ta ce "Yanzu dai duk ba wannan ba, dan Allah mu je daga wancan lungun, mu yi magana" Ya sha kunu ya ce "Ban gane muje lungu ba" "Eh mana, mu je can mu yi magana kar a ganka" "A'a ni ba zan shiga lungu a daren nan ba" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, to ai ba wani abun na ce ayi a lungun ba, magana kawai zamu yi kar a ganka nake tsoro" "Kuma sai ki ce in shiga lungu" "Na shiga uku, sai ka ce wata 'yar iska, kar ka yi mini wata mummunar fassara mana" Viper ya ce "Ke da duk baki yi wannan tunanin ba, ki ka amince da aiki tare da ni, ki ke iƙrarin zaki taimake ni? Ki tsaya ki saurare ni" ya yi maganar fuskarsa ɗauke da matsananciyar damuwa. Duk da bai kasance mai fara'a ba, amma yau akwai damuwa sosai a tare da shi. "Amma dan Allah waye ya nuna maka gidanmu" "Ba wannan ne ya kawo ni ba" "To Allah ya baka haƙuri sir, me yake tafe da kai?" "Nura" ya faɗa a taƙaice. "Waye hakan?" "Ƙanina Nura guduma, bayan mutuwarsa ina duba mahaifiyarsa, sai dai bayan an tsare ni ban samu damar yin haka ba, amma su Walid sukan je amma ba ko yaushe ba, bayan fitowa ta kuma, bani da cikakkiyar nutsuwa, kuma ina matuƙar jin nauyinta ban je ba, ban kuma saka su walid sun je ba" Nabila ta nutsu tana sauraronsa, duk a tsorace take, kar wani ya ganshi, duk da akwai facemask a fuskar sa. "Mijin da ta aura bayan baban Nura ya rasu, shekaru biyu da suka wuce, tana ta fama da rayuwa, ga yaranta guda biyu, a taƙaice dai jiya da su Walid suka dawo daga garin, sun tabbatar mini da 'yar ta aka yi wa fyaɗe ita kuma ba a san in da take ba" Nabila ta zabura ta ce "Kuma?" "Yarinyar da ki ke bincike a kan case ɗin ta, Naja bunkure ta shiga case ɗin" Nabila ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, kalmar nan ko daɗin ji ba ta da shi, dama ita ce? To ba su gano in da maman take ba?" "Ina gaya miki kina tambayata, na baki nan da sati biyu rak, tun da kin ce wanda ake zargi ba shi bane ba, ki fito da mai laifin, ko kuma ni na fito da shi ta ƙarfin tsiya". Cikin rashin fahimta ta ce "In fito da mai laifi kuma ta ina? Nima bulayin nemansa nake ai saboda in wanke client ɗina" "Sai fa kin nemo shi, ko kuma ki tabattar an yankewa mutumin nan hukunci dai-dai da abun da ya aikata" "Amma dai ka san ni lawyer ce ba 'yar sanda ba ko? Jami'an tsaro sune za su yi maka wannan aikin, ni kuma na tsaya na tabattar kotu ta yi adalci" Ya tsare ta da idanunsa ya nuna ta da yatsansa ya ce "Ke zaki yi, ba wanda zai yi sai ke, ki nemo ainihin mai laifin, ko kuma ki bari a hukunta wannan mutumin" "But he's not guilty, he's innocent, ka bari na bi komai a hankali" Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "No matter what it takes, ki binciko ainihin mai laifin nan, an cutar da matar nan fiye da yadda ki ke tunani" Nan ya warware mata ɓangaren labarin sa na Nura, da ba ta sani ba. Rawa ƙafafuwanta suka fara yi, jikinta yayi wani irin sanyi, ta kasa magana. "Ki din ga yi mini uzuri wasu lokutan, ni mutum ne mai tarin laifuka ga mutane, bana son in ga wani a cikin damuwa, ina tsoron ace matar nan guduwa tayi saboda baƙin ciki, ba haka ba ma, voice message ɗin da ki ka kunna mini, sai a yanzu na sake tabattar da muryarta ce, ta tabattar da har gida wanda yayi rape ɗin yaje ya ɗauke 'yar, dan haka ramma tana tare da wanda ya yi mata fyaɗe, kuma Naja'atu Bunkure ta sanshi, ba dan ta tsayawa yarinyar ta shiga case ɗin ba, dan ta bawa mai laifin kariya ne". "Yanzu ka yadda wanda nake karewa ba shi da laifi?" "Na sani, amma dole ki yi wani abu, a nemo yarinyar nan da mahaifiyarta" Nabila zata yi magana, aka haske su da fitilar mota, ta saka hannu ta kare saboda hasken fitilar, shi kuwa yayi ƙuri yana kallon fitilar. Viper ya ce "Ko dai ki gaya masa ya kashe fitilar nan, ko na haɗa idonsa da na motar na ɗauke musu wuta gaba ɗaya" Fitowa yayi daga motar ya ƙaraso in da suke, ya kalli Viper, sai dai a wannan karon ma ya ji wannan faɗuwar gaban. Kallo ɗaya ya yi wa Viper, ya tuna a in da ya ganshi. Ya kalli Nabila ya ce "Arfa waye wannan? Irin wannan samarin kuma ki ka koma kulawa?" Ta kalli Viper sannan ta kalli Nasir ta ce "Yaya me yayi maka ne? Na gaya maka tun waccan ranar he's my client" "Client like how? Shi ne zai din ga biyoki har gida? Get inside kafin na kwaɗeki a wurin nan" Addu'a take Allah ya sa kar Viper ya hasala. Viper ya ciro wata fitila daga aljihunsa, ya haske idon Nasir, ya matsa daf da shi, Viper ya fishi tsawo sosai ya ce "Talk to me, like a man, baka din ga yi mata shouting ba" Ya ja da baya ya kalli Nabila ya yi mata alama da hannunsa na i will call you. Ta jinjina masa kai, shi kuma ya juya zai tafi. "Waye kai?" Nasir yayi maganar cikin dakewa, dan muryar Viper kawai a bar tsoro ce. Viper ya juyo, ya kalli Nabila, da ta bashi tausayi, ban da tana wurin, kuma bai san me abun da zai aikata ka iya haifarwa ba, da sai ya sakawa Nasir iraƙi sannan ya gaya masa waye shi, kamar yadda ya yi wa tijjani yayan yar madara. Ya kalli Nasir ya ce "A man" ya faɗa a taƙaice. Nasir ya waiwaya, ya kalli Nabila zai fara masifa, amma ta zura da gudu ta shige gida. Rufa mata baya yayi, yana masifa har ɗakinta ya bita, yana yi mata bala'i, ganin yana neman ya tozarta ta a gabam mutanen gidan ya sanya ta fara kiran sunam Abba da ƙarfi. Aikuwa Abba ya saukko daga kam benensa yana faɗin "Wai waye yake taɓa mini yarinyar nan, kai Nasir menene haka? Dukanta zaka yi? Shekara Ashirin da biyar sai ka kamata kana duka dan rashin mutunci?" "Abba ba dukanta zan yi ba" "To me ka yi mata take wannan kururwar haka?" "Abba gaba ɗaya Arfa ta canza, ta tsiri wasu irin ɗabi'u na rashin gaskiya, rannan na je ofishin ta, na tarar da ita da wani mutum, gaba ɗaya bai yi kama da mutanen kirki ba, yauma still ta tsaya da wani a waje, maimakon cikin gida tana zance, kamar dai wancan mutumin ne, gaba ɗaya bai yi kama da mutanen ƙwarai ba" Abba ya kalli Nabila ya ce "Arfa, yayanki a kan gaskiya yake, ni kaina shige da ficen samarin nan naki, ya fara isata". "Abba, wallahi ba mutumin banza bane ba, kuma ko mutumin banza ne, ba wata muguwar alaƙa ya gani tsakani na da shi ba, na gaya masa client ɗina ne kawai, amma yaƙi yadda kwanan nan komai nayi sai ya din ga zargina na rasa me nayi masa gaba ɗaya" "A'a Arfa, Nasir yana cikin masu goyon bayanki a gidan nan, tun da har ya magantu, to ya fiki gaskiya, ki san irin mutanen da zaki din ga tsayawa, kuma ki din ga mu'amala da su, yanzu a cikin samarin nan naki, lallai ki duba mai nutsuwa ya zo in ganshi, nima zan fi samun kwanciyar hankali ace kina ɗakinki" Nabila ta yi shiru, Abba yayi ta yi mata nasiha, bayan ya gama ya fita, Nasir ya bi bayansa. Nasir ne ya bi bayan Abba, suka shiga ɗakinsa ya ce "Abba, yakamata ka ja wa arfa kunne, wasu abubuwan take yi kwanan nan, shishishigi a kan wasu abubuwa. Ta sako wannan barrister Naja'atu Bunkure a gaba, kar ta je ta janyo wa kanta wata matsalar" Abba ya ce "To ai ni kaga ban sani ba, ban san me take aikatawa ba wasu lokutan, amma babu komai, zan yi mata nasiha, ka san ba kowane lokaci faɗa yake tasiri ba". Nasir ya ce "Haka na, sannan kuma Abba" "Sannan kuma me, ina jinka" Ya ɗan muskuta ya ce "Abba dan Allah ka bani auren Arfa" Take annurin fuskar Abba ya ɗauke, ya ce "Auren arfa kuma?" Ya ɗan yi shiru yana wasa da yatsunsa. Abba ya numfasa ya ce "Kenan kishi ne ya saka ka shigo kana yi mata faɗa?" Ya girgiza kai ya ce "A'a Abba, ba haka bane ba" "To, Nasir kai ɗa na ne, hakazalia arfa, babu wani banbanci a tsakaninku, dan haka ba zan so abun da zai cutar da ɗayanku ba. Ba zan manta abun da mahaifiyarka tayi mini a kan yarinyar nan ba, kuma haryanzu ina kallon irin ƙiyayyar da take nuna mata, na daɗe da gane kana sonta, amma ina fatan ta samu wanda hankalinta zai kwanta da shi. Muddin ka aureta mahaifiyarka ba zata taɓa barinta ta zauna lafiya ba. Ni bani da matsala da son da kake yi mata, amma ka nemi yardarta, da ta mahaifiyarka tukuna" Nasir ya ce "To Abba, na gode sosai" ya tashi ya bar ɗakin. Nabila banɗaki ta shige, ta rufe ƙofa ta kira Viper. "Yanzu fisabilillahi ka kyauta mini kenan? Ka saka an yi mini faɗa, Allah ne ya rufa mini asiri, dan Allah ka daina zuwa in da nake, gara ka kirani na zo da kaina" "Ki je ki yi tunani a kan abun da na saka ki, ki san abun yi sati biyu kawai ki ke da shi" "Ya kake bani umarni ne a haka, ka din ga lallaɓani mana, why are you always bossy ne? Sai da safe zan duba na ƙara effort, ina iya ƙoƙarina a kai, tauye ni ake yi, ka san ba ni da kowa sai Allah ni, amma ka yi mini addu'a in sha Allah ni zan kawo ƙarshen bunkure" "Allah ya sa" ya kashe wayar. *** Ramma ce ta ƙurawa wayar Abdul ido, ta kalli ƙofar banɗaki, yana ciki yana wanka, ta miƙa hannu ta ɗauka ta bar ɗakin. Bai jima ba ya fito daga banɗakin, sai dai ya nemeta ya rasa a ɗakin, ya fita nemanta, ya tafi kitchen, ya tarar da ita a tsaye a kitchen, da wayarsa a kunnenta cike da rashin gaskiya. Babu tsammanni ta ji ya fizgota, ya kwaɗa mata mari, har sai da ta faɗi ƙasa. Ya duba call logs ɗin sa, ya ga ba a ɗaga kiran da ta yi ba, ya kalleta a matuƙar fusace ya ce "Saboda kin ga ina ɗaga miki ƙafa shi ne zaki tsallake gona da iri, zaki wuce makaɗi da rawa? Bari na koma miki ainihin Abdul ɗina, kuma wannan huakan da ki ka yi, dai-dai yake da sake nesanta kanki da iskar 'yanci. Kuma bari na sake gaya miki, babu wani mahaluki da ya isa ya rabani da ke a duniyar nan ko waye shi, idan kin ga dama ki cigaba da ƙoƙarin lallai sai kin bar gidan nan, zaki ga yadda zan yi da ke"ya fice daga kitchen ɗin ya bar a zaune, hannunta riƙe da kuncinta, hancinta har ya fara zubar da jini, saboda azaba. Ta rasa me ma yakamata tayi, saboda zuwa yanzu zuciyarta ta ƙeƙashe, kukan ma ba iya yin sa take yi ba. Ta ja wuri ta zauna sosai saboda jirin da take ji. *** Sallama take yi a tsakar gida, ta ce "Na shigo ko na koma?" Umma da take ƙofar kitchen ta ce "Idonki kenan arfa? Yaushe rabonki da gidan nan?" "Tuba nake umma, ayyuka ne sun yi mini yawa sosai, amma ayi mini afuwa dan Allah" Umma ta ce "To Allah ya yi jagora" "Amin umma, ina sumayya?" "Tana ɗakinta" Nabila ta nufi ɗakin sumayya, ta sameta tana ta aiki a cikin computer, sallamarta kawai ta amsa, ta mayar da hankali ta cigaba da abun da take yi. "Sumy, dan Allah ki kalleni mana" Sumayya ta ɗago ta kalleta ta ce "Idan na kalleki mai zai amfana miki, ni da nake munafuka?" Jiki a sanyaye ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri, nayi kuskure abun ne ya bani mamaki ya ɗaure mini kai" Tuni hawaye ya cika idon sumayya ta ce "A yadda muke da ke, ban taɓa tunanin wani zai kawo miki aibuna ki yadda ba, ba tare da kin yi bincike ba, amma kai tsaye ki ka danganta ni da kalmar munafunci, baki san wahalar da nake ta yi dan kare rayuwarki ba" Nabila ma sai ta saka kuka ta ce "Dan Allah masoyiyya kiyi haƙuri ki yafe mini, ɓacin rai ne, kin ga sam baki yi mini bayanin komai ba, na samu labarin an saka ki kina bibiyata, dole na shiga damuwa kuma ke baki gaya mini ba" Sumayya ta dubeta ta ce "Waye ya gaya miki ana bibiyarki ta hanyata?" "Ba shi da amfani faɗar, amma dan Allah waye ya saka ki bibiyeni, ki din ga kai masa rahotona?" Sumayya ta kalli Nabila da take ta share mata hawaye, Nabila cikin jin kunya da sanyin jiki, take ta ƙara bawa Sumayya haƙuri. Sumayya ta numfasa ta ce "Honorable indabo ne" Nabila ta waro ido ta ce "Indabo kuma? Meye alaƙata da shi? Me na yi masa?" Nan Sumayya ta warware wa Nabila yadda suka yi da Indabo, lokacin da ya ce taje gidansa su yi program. Hankali a tashe Nabila ta ce "Amma meyasa baki gaya mini ba Sumayya?" "Ya za ayi na gaya miki? Ya ce muddin ki ka sani, zaki iya rasa ranki, kuma na san dole zaki iya aikata wani abu, da zai sanya su yi miki illa, babban abun da ya bani mamaki bai wuce lokacin da muka yi waya da ke ba, ki ka ce kin haɗu da Viper, ya ƙara rikicewa gaba ɗaya, amma na tabattar masa da ƙarya ki ke yi, baki haɗu da shi ba, ina tunanin akwai wani abu a tsakanin sa da Viper, dan cewa yayi, zai yi wa Viper tarko da ke, ya kama shi" Gaban Nabila ya faɗi, gaba ɗaya sai kanta ya kulle. "To tayaya zan zama tarkon da za a kama Viper? Meye alaƙata da shi?" Sumayya ta ce "Ban sani ba, amma dan Allah ki nutsu, kar ki aikata wani abu da zai saka ya cutar da ke, wallahi rashin imanin mutumin nan ya wuce tunaninki, ke hatta a wurin aikina akwai masu saka mana ido, da kin zo sai su kirani, su ce me muka tattauna, har wayar da nake yi da ke suke bibiya shiyasa nake kiranki da wasu lambobin" "Na shiga uku, to ni uban me na yi masa? Sumayya da wace lambar suke kiranki?" "Private number ce, ba sa kirana da lamba" zumbur Nabila ta tashi. Sumayya ta ce "Ina zaki je?" Tayi waje da sauri ta ce "Zamu yi qaya kawai" a tsakar gida ta yi wa Umman Sumayya sallama ta fice. Ƙaramar wayarta ta ɗauko, ta kira Viper, ya ɗaga a rikice ta ce "Kana nan ne, gani nan zuwa" "Ke tsaya mana, ki zo ina?" "In zo wurinka mana ina cikin ruɗani da rashin fahimta" "Koma menene ki nutsu, ki yi mini bayani ina jinki" "Ni ba wani bayani da zan yi maka, kawai zan zo gani nan". Ya ce "Hanya babu kyau, na gaya miki kar ki zo fa" "To a ina zamu haɗu? Rayuwata tana cikin hatsari, ni kawai kana ina, na shga uku" Viper da yake zaune ya tashi tsaye ya ce "Malama ki nutusu ki yi mini magana, kina cikin hatsari kamar yaya?" A fusace ya ce "Na gaya miki hanya babu kyau, ana bibiyarki ko kin manta? Za a fara tracking wuraren da ki ke zuwa yanzu haka. Ki tsaya ki saurare ni. "To ina jinka" "Zan tura miki adress ɗin da zaki same ni, idan kuma ni in zo shikenan" Ta ce "A'a kar ka zo" "Ki samu wuri ki ajiye motarki, zan turo miki adress ɗin in da zaki same ni". "To ka yi sauri" ta cigaba da tafiya a motar, tana waige-waige ko zata ga wani yana bin ta. Ya turo mata adress ɗin da zata same shi, ta ajiye motarta, ta bi adress ɗin. Wurin kamar garden haka yake, ba kowa a wurin, sai manyan bishiyu, ga wurin sanyi mai daɗi. Tana tsaye tana waige-waige, ta ciro wayarta, tana ƙoƙarin kiransa, kawai ta ganshi unexpected a bayanta, sakin wayar tayi ta hau ihu. "Menene?" "Ba tsorata ni ka yi ba, sai ka zo kana wani sanɗa da na zura da gudu fa, ka daina wannan sanɗar". Ya kalleta ya ce "Idan ban yi sanɗa ba, ban amsa sunan Viper ba, sai da aji hucina, ko bayan nayi ɓarna a ankare da na zo wuri, gani menene?" Ta ƙare masa kallo ta ce "Ɗan beauty" Ya tsuke fuska ya ce "Neman me ki ke yi mini?" Cikin damuwa ta ce "Mu zauna, na gaji da tsayuwa" Suka samu wuri suka zauna, ta ce "Dan Allah Viper meye haɗina da Indabo? Shi ya saka sumayya take bibiyata. Ta gaya masa yadda suka yi da sumayya. Ya numfasa ya ce "To me zan yi miki?" "Ban gane ba, ka gaya mini meyasa Indabo yake bibiyata, me nayi masa?" Cikin ko in kula ya ce "Ya za ayi in sani?" "Dan Allah ka gaya mini, kai ma fa ka tambayeni ko na haɗu da shi, me kake ɓoye mini ne? Dan Allah ka gaya mini mana" "Meyasa liti ya rikice ranar farko da ya ganki, ya amince ya kawo ki maɓoyata?" Ta ce "To ya za ayi in sani, ina tambayarka kana tambayata? Ka gaya mini mana" Ya ɗago ya tsura mata ido. "Ka yi magana mana, dan Allah meyasa yake bibiyata, ta ce ya rikice lokacin da ya ji na ce na haɗu da kai" still bai yi magana ba. "Talk please" Zuciyarsa ya ji tana harbawa da sauri, ya girgiza kai ya ce "Kamar na ji kin ce mamanki ta rasu ko?" Turɓune fuska ta yi ta ce "wai ina ta rayuwata, kana tambayata wani abun daban". "Nan gaba zaki so jin dalilin da ya sa na tambaye ki, bana surutun banza ni" Kamar za ta yi kuka ta ce "To ni yanzu ya zan yi da wannan indabon?" Viper ya ce "Ba ruwanki da shi, ni ne dai-dai shi, ki ji da bunkure karki manta, sati biyu kawai na baki ki yi mini aikina" Ta narke murya ta ce "Nawa zaka bani ne da ka sakani aikin, ka san dai ba lawyer gwamanti ce ni ba" "Nawa ki ke so?" "Kai nake so" gabansa ya faɗi, da ya tuna Jauhar sararta ce faɗar haka. "Kina wuce gona da iri" yayi maganar yana kallon in da yake facing. "Daga zuwanka, ka saka DSP ya haɗa ni da Abba, an ce sai na duba samarina na fito da miji, sai ka aureni, tun da duk kai ka janyo koma menene" "Are you serious? Ɗan ta'addan zaki aura kina gidan masu kaki?" Ta ce "Eh mana, ka bani dama na zama yar suganka" Ya ɗora hannunsa a kan ƙirjinsa, ya ce "Ki daina wannan wasan ba na son sa ko kaɗan, haryanzu ina jin motsin jauhar a cikin zuciyata. Idan ki na irin wannan maganganun ji nake tamkar na aikata zunubi mai girman gaske, babu wani abu da zan iya haɗawa da soyayyar jauhar a zuciyata, ki kiyaye wannan ki daina wannan wasan, kar ya zama gaske". "Ba ka son yar sugar kenan sai madara ko?" "Ke ki ka san sugan, ni ba na ta'amalli da shi ma" "To zuma fa ko mazarƙwaila" ya yi mata shiru. Ta tashi ta ce "Kar ka so ni ɗin, amma to ni ya zan yi da wannan indabon bashi da imani, kar ya kashe maka ni" Viper ya ce 'Idan ya kashe ki ya hutar da ni" Murguɗa masa baki tayi, ta kama hanyar tafiya. Sai da tai nisa sannan ya waiwaya yana kallonta. Ita kanta murmushi ta yi, saboda yau ya sake, babu wannan alamar ƙuncin da damuwa a tare da shi. *** Da daddare Nabila tana kan social media, taga wani dogon rubutu, da aka yi, na jinjinawa Naja bunkure, a kan ayyukan ta na jin ƙai. Sumayya na ganin posting ɗin, tayi tagging ɗin Nabila. A take Nabila tayi reposting ɗin post ɗin, tare da caption kamar haka *Lokaci yayi da yakamata mu san haƙiƙanin ayyukan da Bunkure foundation ke gabatarwa, shin da gaske dan talaka take yi, ko kuwa dan rufe ɓarnar masu ido da kwalli kawai take yi?. Mu duba case ɗin yarinya zulaiha, da ya faru shekarun baya, wadda ta fuskanci cin zarafi, daga wani ɗan mai kuɗi, bunkure foundation sun shiga case ɗin domin su tsaya mata, a hukunta shi, amma ƙarshe sai labarin mutuwar zulaiha muka ji, ta kashe kanta ta hanyar shan fiya-fiya, shi kuma wanda ya aikata, yana shekarar ƙarshe na kammala karatun degree a ƙasar Amurika. Bana ƙwaina sai da zakara, akwai tarin hujjoji da nake da su a kan maganata. Jikinta na tsuma, ta yi posting ɗin, ta rufe data. Tayi addu'oin kwanciya bacci, ta kashe wayarta, har ta rufe ido maganganun ta da Viper suka faɗo mata. Lumshe idanunta ta yi, amma maganar sa ta din ga kai komo a zuciyarta. *Ba zan iya haɗa soyayyar jauhar da komai ba, dan haka ki ma daina wannan wasan* Dafe ƙirjinta ta yi, ta ce "Na shiga uku,  tausayin sa kawai nake ji, da wasa nake yi, me nake ji a raina ne?' ta tambayi kanta. Wasi-wasi ne kawai, ta bawa kanta amsa tare da kwanciya. Washegari da safe bayan sallar asuba, ta kwanta ta sha bacci, kasancewar lahadi ce, babu aiki. Sai wajen ƙarfe goma ta tashi, ta yi wanka ta fito ta shirya ta ɗauki wayarta ta kunna. Jerin saƙonni ne suka din ga rige-rigen shigowa wayarta, bayan ta kunna data. Messages kuwa, ga na barrister Habib, ga na summaya. Ƙarƙashin post ɗin ta kuwa, comment ya kusa dubu, da masu kare Bunkure da masu zagin Nabila, kasancewar alherin bunkure galibi mutane suka sani. Ta ɗaga kiran wayar sumayya da yake shigowa, ta ce "Ya ne?" "Nabila daga tagging ɗin ki a post, kin rikita media" Nabila ta ce "Ai makaho ba ya sanin ana kallonshi sai an taɓa shi, bar su su gama haukan da kare ta, ina nan zan saki maganar ramma bayan an kuma zaman kotu". "Amma Arfa kar fa ta yi miki wani abu" "Ba abun da ta isa ta yi, ai ina da hujjoji " "Allah ya ƙara tsare ki, zan cigaba da nemo miki sahihan bayanai a kan ta" Naja ta kalli posting ɗin ta yi murmushi ta ce "Bari na nuna wa yarinyar nan ainihin kalata da take son gani. Kira Nabila ta gani da private number, babu tsoro ko fargaba ta ɗaga. "Wane irin move ne haka, kin san mutanen nan ba za su barki ba ko?" Nabila ta ce "Kai ka bani aiki ka ce nan da sati biyu, aka yi sara a kan gaɓa, sumayya ta yi tagging ɗina a kan post ɗin, na ga ya dace na tofa wani abu". Viper ya ce "Shikenan, amma ki shirya matakin da za su ɗauka a kanki" Nabila ta ce "Ina da kai ai, idan na je aiki zan kiraka" Nasir ne ya faɗo ɗakin ta ya ce "Nabila, wai meyasa baki da hankali ne" Ta kalleshi ta ce "Me nayi kuma?" "Ban ja miki kunne a kan Naja'atu Bunkure ba? Kin je kin tsokanota, gashi an fitar da sanarwa hukumar DSS suna nemanki, an shigar da ƙararki for defomation of character". Ayshercool 08081012143 62 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Ta ce "Ban gane ba, su DSS ɗin uban me na yi musu suke nema na, kamar wata 'yar ta'adda". "Shut up, ina magana kina yi mini gatsali, abun da nake ta ankarar da ke kenan ai, matar nan tafi ƙarfin ki, ba sa'ar yinki ba ce ba, amma saboda zunzurutun taurin kai, da zigar da ki ke ɗauka, kin cigaba da abun da ki ka ga dama, da yake ba kya son zaman lafiya" "Ina son zaman lafiya DSP, kuma duk abun da nake yi da hujja nake yin sa, dan haka a gaban kotu yakamata ta ƙalubalance ni, ba wurin DSS ba, uban me nayi mata?" "Look arfa, matar nan ba zata bi abun da doka ta tanada ba, dan tana tsoronki, koma menene za ta yi shi ne, dan kawai ta tozarta ki, ta nuna miki ke ɗin ba kowa ba ce ba, kuma babu abun da wani ya isa yayi. Ko hurumin DSS ne su kama ki, ko ba hurumin su ba ne, za su yi abun da ta ce ne, kuma babu mai ƙwatarki" Kawai Nabila ta saki murmushi ta ce "Ai DSP duk wanda ya ce ayi wasan jifa, ya san me ya taka ne? Dss ai ba lahira bane ba, a yadda nake ji na yanzu, hukuncin Allah shi ne abu mai razanarwa da firgitarwa a gare ni. Ban fara wasan ba, sai da na tabattar da ingancin ƴan wasa na. Ita taƙamarta tana da manya a sama, da zasu tsaya mata, abun da ta manta da ita da manyan banzan nata shi ne, ƙanan na ƙasa su suka zama tsaninsu wurin zuwa ƙololuwar in da suke tafka tsiyar, daga zarar na ƙasan sun yi bore, na saman dolennsu su shiga hankalinsu, ita ta iya Black market ni ta hanyar shari'a zan nuna mata kuskurenta legally" "Shut up a beg, uban me ki ka taka, mara hankali kawai, zaki tayar wa da mutane zaune tsaye" tayi masa shiru ya fice yana sababi. Nan fa yan gidan, suka samu topic of discussion, ko a jikinta, ta gama shirinta tsaf, Baba magajiya ta iske a falo, ta ce "Yauwwa arfa, dama ke zan zo na kira, babanki na nemanki yanzu da gaggawa". Duk da sauri take yi, amma ta nufi ɗakin Abba, ta iske shi da shi da Nasir, hankalinsa a tashe. "Arfa, me ki ka je ki ka aikata? Yayanki ya ce kin yi posting a social media kin tayar da tarzoma jami'an tsaro suna nemanki" Nabila ta ce "Wallahi Abba ban tayar da tarzoma ba, gaskiya kawai na faɗa, kuma haryanzu a hukumance ni ban ga cewar DSS su kama ni ba" "Ƙaniyarki da ke da hukumar, amma dai kin san ni yanzu ba da bane ba da zaki je ki tsokano mutane ko, tsokanar taki ma, ki ka kasa yin dai-dai da ke, sai in da zaki sha wahala, haka kurum ki tayar mana da zaune tsaye, muna zaman lafiya a ga DSs sun yi mana dirar mikiya a gida, kamar wasu yan ta'adda". "Abba ba su da hurumin kama ni, ban ɓata wa kowa suna ba, gaskiya kawai na faɗa" "Rufe mini baki, ko na saka ki tsallen kwaɗo yanzun nan, mara kunya fitsararirriya". Wayarta ce take ringing, ta ce "Bari na ɗaga waya" "Hello yaya Habib" "Nabila kina ina ne?" "Ina gida, yanzu zan fito wurin aiki" "Maza ki hanzarta ki ƙaraso, na ga wani rumors yana yawo, a kan posting ɗin da ki ka yi jiya, wai Dss suna nemanki, duk da ba officially na ga sanarwar ba, magoya bayanta ne suke ta zuzuta maganar, maza ki ƙaraso mu riga su ɗaukar mataki" "To Barrister, gani nan in sha Allah" ta sauke wayar ta ce "Abba daga law firm ɗinmu ne, bari na tafi" "Ki tafi ina, an ce ana nemanki?" "Eh zan je in ji me za su ce ne" Abba ya kalli Nasir ya ce "Ka kai ta law firm ɗin na su, duk yadda ake ciki, ka kirani, zan je na ga likita sai na biyo" Sam Nasir ba haka ya so Abba ya yi wa Nabila ba, ya so ya ja mata kunne sosai, ya taka mata burki a kan abun da take yi, amma bai yi hakan ba. Suna tafe a mota, ba ta kula shi ba, sai waya take yi da sumayya da murtala, sumayya ta ce zata ƙarasa law firm ɗin su Nabila. Tana sauke wayar sumayya, kira ya shigo, an rubuta Confidential a kan lambar. Ya kalli Nabila, ya kalli wayar, kasancewar Bluetooth ne a kunnenta, ya sanya ta amsa dan kaucewa zargin sa. "Hello boss" Viper ya ce "Ya ake ciki? Sun kama kin ne?" "So ka ke su kamanin kenan?" "Am asking? Ya ake ciki?" "Eh, ba su da hurumin kama ni, yanzu ina hanyar law firm ɗin mu ne, Oga na a wurin aiki ya ce maza naje, a riga su ɗaukar mataki". "Ok, amma you over react, na so ace a sannu ki ka bi abun, amma yanzu zamu raba hankalinsu biyu, zan yi wa Indabo aike, hakan zai sanya su kasa tsayar da hankalinsu wuri guda" Ta kashingiɗa da jikin seat ɗin mota ta ce "Aiken me?" "Ke da waye a motar nan?" "Meyasa ka tambaya?" "Akwai rashin sukuni da tsoro a cikin maganarki, ke da wayar" Nabila ta waro ido ta ce "Kai ya aka yi ka gane, vi.... Saurin katse maganar tayi, da tuna katoɓarar da kusa tafkawa. Tayi gyaran murya ta ce "Zamu yi magana anjima, yanzu ina cikin zullumi jami'an tsaro za su kama ni, ka bari na yi salati na nemi agajin Allah" Viper ya ce "Ok" ya kaste kiran. "Da wa ki ka yi waya?" Ba tare da ta kalli Nasir ba, ta bashi amsa da abokin aikina ne. *** Ramma ta takure kanta sosai da sosai,  tun da Abdul ya dake ta, ya fice daga gidan ba ta sake ganinsa ba, itakaɗai take kwana take tashi, kuma ya ɗauke wayar da ya bata, da take kiransa a ita, hatta system ɗin sa guda ɗaya da yake ajiye mata, yana koya mata computer ko tayi kallo, dan har fina-finai na hausa, yake yi mata downloading dan su din ga ɗebe mata kewa, gaba ɗaya ya haɗa ya kwashe, ƙofar da zata fito da ita, ta sauka daga kan bene ma zuwa falon ƙasa, duk ya haɗa ya rufe. Sam ba ta ko iya cin abinci, damuwa ta dawo mata sabuwa fil, ta rasa abun da yake yi mata daɗi baki ɗaya. Tana zaune bayan sallar isha'i a bedroom, ta ji ya buɗe ƙofa ya shigo, a razane ta waiwaya ta ɗan ja da baya. Ya ɗan tsura mata ido, sannan ya mayar da ƙofar ya rufe, ya nufi in da take hannunsa da leda. Ya ajiye ledar, sannan ya zauna a kusa da ita, amma ta sake ja da baya. "Guduna kuma ki ke yi yau?" Da ya motsa sai ta zabura, dan gani take dukanta zai kuma yi. Shammatarta yayi, ya janyota jikinsa, ya rungumeta a ƙirjinsa ya ce "Am sorry please, ki yi haƙuri dan Allah" ta yi shiru ba ta ce masa komai ba. "Ki yi haƙuri, tsantsar tashin hankali da na shiga ne, ya sanya na aikata miki abun da nayi, bana son gardama da taurin kai, tun da ki ka ga na ajiyeki, duk da irin son da nake yi miki, da magiyar da ki ke yi mini, ban mayar da ke gida ba, akwai matsala ne, mamanki ina zuwa wurinta, na tabattar mata da kina cikin ƙoshin lafiya, abin da ki ka yi shirin yi, barazana ne ga rayuwarki. Wallahi regret ne ya hanani dawowa tun da na fita na nutsu, gaba ɗaya nake cikin damuwa, amma ki yi haƙuri dan Allah" Tayi lamo a jikinsa, amma taƙi magana. "Rahama talk dan Allah, ki yi mini magana mana ko na ji daɗi dan Allah ki yi haƙuri ki yafe mini, son da nake yi miki ne ya sanya na ga abun da ki ka aikata barazana ne ga cigaba da kasancewarmu tare, ki yafe mini" ai kamar gunki, taƙi cewa uffan. Ya ɗago fuskarta, yana kallonta, amma ta sunkuyar da kanta ƙasa. Ya janyo ledar gabansa, ya buɗe tsire ne fal a ciki, ya ce "Ki ci abinci, duk kin faɗa kwana biyu, dan Allah ki yafewa Abdul ɗinki, ba zan ƙara dukanki ba" Ta saka hannu ta share hawayenta ya ce "Yauwwa babyna, ai na zaki yafe mini, kina da yafiya shiyasa nake ƙara ƙaunarki Rahama, Allah ya yi miki albarka ya shirya miki ni" da ƙyar ya din ga bata abincin a baki, ta ci kaɗan ta tashi, sam taƙi sakar masa fuska. *** Nabila suna zuwa law firm ɗin su, Barrister Kabir ya balbaleta da faɗa, Nasir ma ya taya shi, akan kasadar da ta yi. Duk da Nabila ba ta son faɗa a rayuwarta, amma ko a jikinta, ta maze tana cunkusa baki. Barrister Habib ya ce "Dan Allah ku yi haƙuri haka, aikin gama fa ya riga ya gama, ta riga ta aikata, sai a san abun yi, kuma wannan duk ba abu ne na tayar da hankali ba, in dai mutum yana da gaskiya, ai faɗa ba nasa bane ba. Nabila shigo office mu yi magana. Barrister Kabir ya ce "Naga kamar goya mata baya kake yi Habib, idan kuka janyo abun da ba zaku iya ba, to ku tsaya can, kar ku raɓa ni a ciki" "To barrister idan ba a goya mata baya ba, kware mata baya zamu yi, ma'aikaciyarmu ce, tayi abun da wani bai yi yinƙurin yi ba, ai kamata yayi a duba, idan akan gaskiya take, a ƙarfafeta, shigo mu yi magana" Nabila ta shiga cikin office ɗin sa, ya ce "Good girl, i like your confident, a lady of her words, kin dage sai kin cimma burinki a kan matar nan" Ta ce "Yanzu dai ba wannan ba, meye abun yi, kafin a zo a kamani, nima su saka a kaini prison a ajiyeni babu Shari'a kamar yadda suka yi wa Viper" "Suka yi wa Viper ita da wa?" Nabila ta ce "Oho mata, shi ma wannan case ɗin ina nan zuwa kansa, zata gane bata da wayo ai" Yayi murmushi ya ce "Ba wannan ba, na yi wa Bashir ma magana, yana hanya, zamu yi maza mu shigar da ƙara, a kan lallai kotu ta dakatar da kamun da aka ce Dss su yi miki idan ma da gaske zasu kamakin, ba su da wannan hurumin, sannan su daina yi miki barazana dan kin faɗi albarkacin bakinki" "To ayi sauri ayi, dan wani update ɗin zan saki, da ni take zancen" Duk da hantarar da Barrister Kabir ya yi wa Nabila, tare da shi, da sauran lawyoyin law firm ɗin, suka haɗu suka tattara bayanai, da hujjoji da za su kai kotu, dan hana kama Nabila. Suna can suna ta ƙoƙari, Nabila suka keɓe da Sumayya, ta tura mata videon yaron da ya ketawa zulaiha haddi, a cikin abokansa a ƙasar amurka. *Wannan shi ne Najib, wanda ya keta wa yarinya zulaiha haddi, har ta kaita ga rasa ranta, a shekarun baya, shin ina shari'ar ta tsaya? Ko ya fi ƙarfin doka ne, dokar a kan talaka kawai take aiki? Kwana kwanan nan, mun ga yadda labarin wani matashi ya cika dandalin sada zumunta, a kan yadda aka tsare wani matashi shekara goma sha biyu, a gidan gyaran hali, bisa zargin sa da aikata fyaɗe, sai bayan shekaru goman nan, a ziyarar da wani bawan Allah ya kai gidan, ya tausaya masa, ya tsaya masa aka cigaba da yi masa shari'a har aka gano ba shi da laifi, saboda shi talaka ne ya sanya Bunkure foundation ba ta shiga ire-iren cases ɗin nan, sai dai na mata kawai? Me zai saka ace mata kawai foundation ɗin take tsayawa ban da maza? Anya babu wata maganar a ƙasa?. Wannan ra'ayina ne a matsayina na ƴar ƙasa, wanda yake da ja, a gaban Alƙali zai ƙalubalance ni, ba wai a din ga yi mini barazana ba* tayi posting ɗin tana murmushi, ta ce "Sumy na zama celeb fa" "Zaki ci ƙaniyarki ke da celeb ɗin, kina kan sirɗin duniya kina rashin mutunci, akwai buƙatar mu nutsa sosai, mu cigaba da samo hujjoji, dan mutane su yadda da abubuwan da ki ke tonawa, dan na san haryanzu akwai masu tantama a kai" "Haka ne, wannan kuma sai idan muka sake tsayawa a gaban kotu a kan case ɗin ramma" "Allah ya ƙarfafeki, ya baki sa'a" "Amin godiya nake masoyiyya" Sumayya ta ce "Amma Nabila ya za ayi da Indabo ne? Ina tsoron mutumin nan, kin ga kuma shi babba ne, tun a lokacin na so na kai report, amma yayi mini kashedi a kan haka, babu ma wanda zai yadda da ni, saboda muƙaminsa" Nabila ta ce "Rabani da zancen wannan mutumin, ni yanzu wannan matar ce a gabana, shi kuma akwai dai-dai shi" "Wa kenan?" Nabila ta basar da zancen ta shiga wani. *** "Indabo ka yi wani abu a kan lamarin nan, lallai a kama yarinyar nan a koya mata hankali, ban san da me take taƙama ba, ba a taɓa samun tsageran da yayi mini abun da take yi mini ba, idan fa asirina ya tonu, kuma naku ya tonu wallahi" "Kar ki damu, muke da ƙasar fa, babu abun da ta isa tayi, na riga na bayar da order da ta kamata" Ta kashe wayar, cikin fushi, tana mamakin ƙarfin halin Nabila, manyanta ma sun gaji sun ƙyaleta, ba a iya ja da ita, amma yanzu yar ƙaramar alhaki ta sakota a gaba. Indabo ya daddana wayarsa, ya saka a kunnensa, "Barka da wannan lokaci distinguish senator" "Barka dai, ya ake ciki ne maganar yarinyar? Na ji kun ce Dss su kamata ya ake ciki, dole fa a toshe duk wata hanya da za a tonawa bunkure asiri dole a tosheta". "Sir yarinyar nan fa tana da wayo, kuma tana da wanda suka tsaya mata, ta tafi kotu, ta ce lallai a hana kamata kuma ba wanda ta ɓatawa suna, sai dai bunkure ta ƙalubalanceta a gaban shari'a" Ya numfasa ya ce "Haka ta ce? Wane alƙalin ne? Wace kotun ce zan bayar da umarni a bi umarninta a ƙi bin nawa" "Honorable ka gane wani abu, abun nan fa ya haɗa da social media, ba zai yiwu mu yi abu gabagaɗi ba, su kansu ƙungiyar lawyoyin ba zasu bari ba, kuma madam tana da magauta a cikin su kansu lawyoyin, za su iya taimaka mata, idan aka yi over reacting, to asirin da ake gudun tonuwarsa zai tonu" Indabo ya ce "Shikenan, na fahimta". *** Madaki ya kalli ƙafarsa, ya kurma wani irin uban ihu, tamkar mahaukaciya, Lakwari ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri ka daina wannan ihun, hakan ba mafita bane ba". "Ka rabu da ni nayi ihun nan, sai na kashe yaron nan, abun kunya ne ace kamar ni, ƙasƙantaccen maƙiyina, ya ga bayana ya sabauta rayuwata, sai na kashe mai zamani na ƙarar da zuriyar su*. Lakwari ya kalli ƙafar madaki, ta kumbura kamar mai dundumi, sai wani irin koren ruwa ne yake fita daga cikin ciwon ga wari da yake yi, ga maganin da aka bashi, aka ce ya din ga sakawa, ya sanya raunin ƙara jagwalgwalewa, ko iya taka ƙafar baya yi. "Madaki, ka yi haƙuri mu je asibiti a duba ƙafar nan, ni fa ban ga alamar ciwon nan yana warkewa ko zai warke da haka ba, ƙara jagwalewa yake yi". "Idan na je asibiti asirina tonuwa zai yi, idan lakwayen nan suka san alkadarina ya karye na shiga uku, kai ka san ta'adin da na yi ai" "Haka ne, amma duk da haka yakamata muje asibiti a duba ƙafar nan, tun da babu sauƙi a ciki" ya din ga lallaɓa madaki har ya samu ya amince. Viper yana tsaye tare da su liti, ɗan mama ya shigo, Viper ya ce masa ya ake ciki? "Komai normal, saƙonka ya isa cikin aminci da kwanciyar hankali. Na shiga area na yi bincike sosai, babu wanda ya san in da madaki yake, amma an tabbatar mini da yana jinya, kuma lakwari ne a tare da shi, sai dai ba a san in da yake ba" Viper ya zaro russia, ya jujjuyata a hannunsa, ya kalli ɗan mama ya ce "Ka nemo duk in da suke, ina son ka samo target mai kyau, in da zan ritsa lakwari, na san ƙafarsa ɗaya ta mutu zuwa yanzu, zan hari wani wurin na daban kuma" "Sai da kai ubangidana, abun da ka ce shi za ayi" "Bari mu ga respond ɗin da Indabo zai yi, idan ya ga saƙona" *** "Hello, barka da wannan lokaci" "Yauwwa barka sir" "Ina magana da justice maijidda ɗan rimi ne" "Eh nice" "Good, ina fatan kin gane mai magana?" Tayi murmushi ta ce "Ya za ayi na ce ban gane ba sir, na gane" "Masha Allah, akwai ƙara da wata yarinya da sauran lawyoyi suka shigar gabanki, barrister Nabila Yusuf maitama, a kan ki hana Dss kamata, da kuma hana yi mata barazana, ki bi tsarin doka ki yi abun da ya dace, na san dole za a nemi ki yi wani abu ba dai-dai ba, idan ki ka yi akasin abun da doka ta tanada, zai iya janyo wa ayi seizing license ɗinki, nima umarni aka bani daga sama" "In sha Allah sir, zan yi abun da ya dace ba tare da son rai ba, na gode sosai da sosai" Ya ce "Yauwwa" A media kuwa aka cigaba da samun musayar ra'ayi, kowa da abun da yake faɗa, waɗanda bunkure foundation ta cutar, suma suka samu damar bayyana ra'ayoyin su, duk da mutanen da suke ganin hassada ta sanya ake yi wa bunkure hakan sun fi yawa. Bayan Bunkure ta gama sakankancewa, ta gama da babin Nabila, sanarwa ta fita, kotu ta haramtawa Dss kama Nabila, ko yi mata barazana a kan abun da take aikatawa, a matsayin ta na ƴar ƙasa, tana da ƴancin faɗar albarkacin bakinta. Indabo kuwa yana cikin majalisa, ya zauna, ya fara ƙoƙarin buɗe envelope ɗin da aka bashi, aka ce an aiko masa da ita. Ya buɗe ta ya ƙara ciro wata ƙarama a ciki. Hoton ciki ya kalla, Simon ne tare da Viper a cikin hoton. Simon yana daga cikin yaran da Indabo ya lalatawa rayuwa, kuma ya zama ɗaya daga cikin masu yi masa hidima, a wannan gidan da suke sheƙe aya da shi da ire-iren sa, da suka sanya neman duniya a gaba. Wanda shi ne ya kuɓutar da Nura guduma daga gidan, ya saka shi a mota, ya haɗa shi da wani ya kai shi kano. Shi kuma ya gudu daga gidan, indabo ya bayar da cigiyar a nemo simon, ya bayar da kwangilar a kashe shi, aka tabattar masa da an kashe shi, amma hoton ya nuna masa kwanan nan aka ɗauka. Cikin tashin hankali yake sake kallon hoton, tabbas na kwanan ne hoton, saboda Viper ya ƙara girma, fuskar nan babu annuri a tattare da ita ko kaɗan. "Simon yana raye kenan?" Ya tambayi kansa, ya juya bayan hoton ya ga an rubuta Viper da jan abu. Bai san ya tashi tsaye ba, sai da na kusa da shi ya ce "Honorable, ya aka yi ne? Me kake gani?" "A'a ba komai, ulcer ta ce ta tashi" ko izini bai nema ba, yayi waje daga cikin majalisar kamar babbar rigarsa zata harɗe shi ya faɗi. *** "Assalamu alaikum, Assalamu alaikum ba kowa a gidan ne?" Walid ya ce "Wa'alaikum Salam, barrister yau ke ce?" "Ina wuni Yaya walid" Yayi murmushi ya ce "Lafiya ƙalau, yau kin tuna mini da ƙanwata jauhar" Ta ce "Allah sarki, Allah ya sa tana aljanna" Ya amsa da "Amin" "Ina ogan yake?" "Ya tafi caji" Ta ɗan yi turus ta ce "Caji kuma, kamar wani power bank?" Yayi dariya ya ce "Ya ce, ya fita shan iska yana wurin wancan dutsen" Ta ce "Ok, bari na je" "To Allah ya sa yana ƙasa, ba saman ya hau ba" Nabila ta ce "Idan ma saman ya hau, zan bi shi" Da tazara daga gidan zuwa dutsen, duk da daga gidan sai ka zata taku kaɗan zaka yi ka ƙarasa. Daga nesa ta hango shi, a zaune a ƙasa-ƙasa, ta hango tashin hayaƙi a wurin. Ta ƙarasa da ƙyar, dan duk ta gaji, kwali guda ne a gabansa, ta ƙarasa ta kai hannu ta ɗauke, caraf ya riƙe hannunta. Tsorata tayi, dan cikin sanɗa ta ƙarasa wurin, amma har ya ankare da ita ya hanata ɗauka. Ta haɗe rai ta ce "Sakar mini hannu, nan ka gama cewa zan saka a lungu, shi ne zaka wani riƙe mini hannu?" "Ni na kawo ki? Ban ce ki daina zuwa ba ma?" "To ko kirana ba ka sake yi a waya ba, idan ma an kama ni, ko ma menene ya same ni, ba ruwanka ko?" Tari ta fara yi, saboda hayaƙi, sakar mata hannu ya yi, tayi sauri ta ɗauke kwalin sigarin da ashanar, ta tura a jakarta. Satchet ɗin maganin da ya leƙo a gefen aljihunsa, shi ma ta ɗauke, tana mita "Wallahi Allah ya hore maka taurin kai, wannan shaye-shayen ne ba zaka daina ba ko?" Ya ƙura mata ido, saboda jin tana ƙamshin turaren florie irin na 'yar madara. "Ina magana kana kallona, baka tausayin lafiyarka, yanzu duk ƙoƙarin jauhar a kanka ya tashi a banza, yawaita yi mata addu'a, istigfari da mayar da hankali a kan addu'a, shi zai rage maka damuwa, amma baka ji, kullum cikin hayaƙi, da shan miyagun ƙwayoyi" "Faɗa fa ki ke yi mini" "Au kar na yi maka? Ka daina mana da na yi maka mana, wannan abubuwan da kake yi ba shi yake nuna halaccinka a gareta ba, ka daina abun da ka ke yi, ka zama mutumin kirki, shi ne cikar halaccinka a gareta" Kawar da kansa gefe yayi a hankali ya ce "Angry bird" "Ni ce bird ɗin? Wallahi ni ba tsuntsuwa ba ce ba, da ba ka neme ni ba, ni gani ai na zo, ba a kama ni ba fa" "Dama na san ba za a kama kin ba ai" "Haba ya aka yi ka sani?" "Bani wayarki" ta ciro wayarta ta miƙa masa. Ya ciro tasa ya danna, sannan ya saka a kunnensa. Muryar P.A ta fito rangaɗau a waya ya ce "Hello" Viper ya yi shiru, bai ce komai ba. Ya sake cewa "Hello", still bai yi magana ba. "Waye ne ya ɓoye lamba yake kirana, idan ba za ayi magana ba, zan kashe, waye?" "Mai zamani ne" waro ido P.A yayi ya ce "Wane mai zamanin?" "Zuwa yanzu, na san saƙona ya iske shi, ya shirya, zan bayyana a lokacin da bai yi tsammanina ba, kuma ya daina wahalar da kansa a kan lallai sai an kamani, ko da an kama ni, nafi ƙarfinsa, ya kuma jirani aikena na biyu" ya katse wayar yana ajiyar zuciya. "Kai, Oga kana burgeni, ka din ga acting kamar a film ɗin indiya hausa, wai dan Allah, a ina ka ko yi wannan halin naka?" Ya jefa mata wayarta jikinta. "Amma wait, wai ne ka ke yi a wayata ne baka gaya mini?" "Yaushe zaki fara shari'ata?" Nabila ta ce "Shari'arka akwai sarƙaƙiya boss, sonake na gama da ta ramma gobe in Allah ya kaimu zamu koma kotu." Ya jinjina mata kai. "To zaka fara bani kuɗin aiki ai, ka ɗan ragen wani abu, na din ga zuba mai, tun da na je fa aka nuna mini file ɗin ka, nake ta up and down, ina tattara abun da zan tattara. In sha Allah zan zama sanadin daina zubar hawayenka" "Dama kuka nake?" "A'a murna ka ke yi" Ya girgiza kai ya ce "Ko matata da muna tare, ta daɗe kafin ta iya kallona ta yi mini magana, balle ta yi mini baƙar magana, amma ke kin mayar da ni kamar wani sa'anki, har hantarata ki ke yi" "Ni ɗin ce na rainaka? Ni na isa wacece ni? Amma dan Allah sweetheart meyasa ka kusa kashe ni ranar farko da na zo wurinka?" Ya ɗago ya kalleta ya yi shiru. "Ka amsa mini dan Allah" "A lokacin ai kamar mahaukaci nake shiyasa" Ta girgiza kai ta ce "A'a, wani abu na din ga gani a idonka, da na rasa menene? Dan Allah meyasa?" "Ke ban sani ba, tashi ki bar wurin nan" Ta noƙe masa kafaɗa tana kallon idonsa, abun da ya tsana. Yayi tsaki ya kawar da kansa gefe. Turare ta ɗaukko a jakarta, ta toshe hancinta, ta fesa a wurin. Ba shiri ya waiwayo yana kallon hannunta. "Gashi yanzu na saka ka waiwayo ai, gashi saya maka na yi" ya karɓi turaren, ya din ga juya shi a hannunsa yana kallo. Ta na ƙoƙarin ɗaga wayar da ake yi mata, ta ga hawaye na ɗiga a hannunsa. Sai jikinta yayi sanyi gaba ɗaya. "Haba mai babban suna, a yanzu fa kuka ba naka bane ba, wanda ka yi ya isa, mu cigaba da addu'a da ƙoƙarin tattara shaidun da zamu shiga kotu da su, dan Allah ka daina bana jin daɗi. "Da jauhar na raye, da yanzu na san ta kammala law school, maybe ta haifi yaronmu na biyu ko uku, ina da tarin burika a kanta, na kyautata rayuwar ta, ta ji daɗi ta huta, saboda wahalar da ta sha a rayuwarta, amma wauta ta da rashin hankali, ya sanya ta mutu ta bar ni a duniyar. Lokacin da duniya ta yi watsi da ni, ake yi mini kallon mara amfani, ta rungume ni, ta karɓi ƙaddararta, ta kula da ni, a lokacin da nake ƙoƙarin kyatata ratuwarta na fara bata kulawa, lokacin da na fara gano haske yana tunkaro rayuwarmu, ashe yayi daidai da lokacin da zan yi girbin ya mummunar hanyar da na zaɓawa rayuwata, na rasata" yayi maganar yana ƙoƙarin mayar da hawayen sa, amma suka cigaba da zuba, kamar an kunna famfo. "Viper, ka yi haƙuri, Allah ya ambaci masu haƙuri a wurare daban-daban a alƙur'ani, tare da yi musu bushara. Viper Allah ya fi kowa so da kishin bawansa, wataƙila mutuwar jauhar a wannan lokacin shi ne mafi alkhairin ta, a duk buɗe ido muka yi muka ganmu a duniya, dan haka ba zamu tsarawa Allah yadda muke son kasancewa ba a duniya. Ba kowa Allah ya tsarawa jin daɗi a duniyar nan ba, ai dama ita duniyar kurkukun mumini ce, aljannar kafiri. Wani ga jin daɗin yana cikinsa a zahiri, amma a baɗini rayuwar kawai suke yi mara ma'ana. Yanzu tsohon ubangidanka ga duniyar ya samu, yana jin daɗin amma nauyin zunubin da yake aikatawa ba zai taɓa barinsa ya rayu cikin kwanciyar hankali ba. Ba sai mutum ya samu wadata dan ya sha wuyar rayuwa, shi ne tabbacin Allah yana son sa ba, duk tsananin rayuwa da ka ke ciki, idan har ya barka da imaninka, kuma ka yi kyakywan ƙarshe, wallahi ya fiye wa ɗan Adam duk wani abun more rayuwa. In dai ana samun aljanna a biyayyar iyaye, da biyayyar aure in sha Allah Jauhar ta samu" ya jinjina kai yana cigaba da zubar da hawaye. Ta bashi handkerchief ɗin ta, ta ce "Share hawayen haka, kaga ni ma ka saka ni kuka, bana iya jure in ga mutum a cikin damuwa ko yana kuka, alhalin ba zan iya yaye masa damuwar sa ba. Yanzu ni kaina, duk abubuwan da nan da nake yi, ƙarfin hali nake yi, zuciyata akwai wani ciwo da yake addabata, ina kuka iya yi na wasu lokutan, sai dai babu yadda na iya, da abun da ƙaddara ta zana mini" tayi maganar ita ma tana kuka. Ya ɗago ya kalleta, ya motsa baki, yana son ya faɗi wani abu. Ayshercool 08081012143 63 Ta share hawayenta, ta ɗaga kanta ta ga ita yake kallo ta ce "Ka ce mini ka yi wa Indabo aike, me ka aika masa?" "Hotona ne" "Hotonka kuma?" "Eh, hotona ne da ni da wani yaronsa da yake zaton ya saka an kashe masa shi" Ta zaro ido ta ce "Wai shi mutane nawa ya kashe kenan a rayuwarsa?" Ya rausayar da kai ya ce "Mutane sun ɗauki duniya fiye da yadda ki ke tunani. A baya bayan matsalar da nake fuskanta a gidanmu, fatan da nake yi kullum, Allah ya bani abun yi, ko iya abinci in din ga samu ina ci, sai da na haɗu da uban gidana dodo, ya haska mini duniya da in da mutane suka saka gaba. Da na so na yi kuɗi da yanzu ni hamshaƙin attajiri ne. A lokacin da jauhar take ciyar da ni, da fari babu abun da yayi mini zafi, gani nake kawai auren dole aka yi mini, sam ba ta gabana, sai dai abun mamakina da ita, duk abun da zan yi mata bata jin haushi, naga yadda take sana'a tuƙuru iya yin ta, dan kar mu zauna da yunwa, daga baya nayi noticing idan abinci ba zai isa ba, sai ta bani ita tayi kame-kame ba ta ci ba, a lokacin ba wai dan tana so na bane take yi mini haka, ta rungumi ƙaddara ne, kuma tana tausayina. Daga baya sai na fara jin kunyarta, lokacin da ta roƙi na sayo mata omo, naga responsibility ɗina, amma na zuba mata ido take yi, kuma bata taɓa nuna mini ta gaji ba. Sai dai a lokacin ba ni da wata sana'a sai sayar da wiwi da ƙwayoyi, yadda take yi mini addu'a Allah ya wadata ni da halal, ya nesanta ni da haram, ya sanya na ji ba zan iya ciyar da ita da kuɗin wiwi ba. Sai a lokacin naga ashe, bayan mutuwar Sadik kukan daɗi nayi, da na ce na rasa sana'a, dan a lokacin na din ga faɗi tashi, saboda kar na ciyar da ita da kuɗin ƙwaya. Da in ciyar da ita da wannan kuɗin, gara na dawo na maze na ce bani da kuɗi, na san ba ɗaga mini hankali za ta yi ba. Gashi lokacin tana ta ƙoƙarin rabani da hulɗa da Indabo, wataran idan na ga wahalar tayi mata yawa, haka nan nake zuwa na tsitsiye Indabo ya bani kuɗi. Zuciyata ta sha raya mini, na faɗa mummunar hanya, na samu kuɗi saboda jauhar ta huta, bana nuna mata hakan a zahiri, amma zuciyata kullum a takure babu daɗi. Duk da tsamin alaƙar da ke tsakanina da mahaifina, sai da na din ga jin tamkar na je na ce ya bani aron kuɗi nayi jari, amma na kasa, mussman tuna halin matarsa. A lokacin da tausayinta ya fara zama tsananin so a cikin raina, da tana uzzura mini ko yi mini tashin hankali, da babu abun da zai hanani kauce hanya, dan yahoo zan fara, kuma kuɗi zan samu sosai da sosai, haka nan na san in da zan yi dillancin miyagun ƙwayoyi a tsakanin manyan mutane, har da ƙasashen ƙetare na samu kuɗi, amma ban taɓa burin tara kuɗi da mummunar hanya ba. Ina ga lokacin da tayi ɓari ne, bani da wasu kuɗi sai na wiwi, shi ne aka yi mata magani da su, amma banda haka, ban taɓa ciyar da ita da kuɗin ƙwaya ba". "Viper, labarinku abun tausayi, kuma gwanin daɗi, Allah ya bani ikon zama kamar jauhar, ina sonta sosai" "Sai dai ki kamanta, ba zaki iya ba, ke mafaɗaciya ce, matata kuwa kan tayi faɗa sau ɗaya ana daɗewa, shiyasa nake kiyaye abun da zai ɓata mata rai ya sa tayi fushi, har ta yi faɗa. Na gode sosai da saka ni kuka da ki ka yi" "Saka ka kuka kuma?" "Eh, tun da na rasa jauhar, ban zubar da hawaye ba" "Ai kai jarumi ne, bari na tashi na tafi gida, ka yi mini addu'a, gobe in Allah ya kaimu zamu zauna a kotu" Ya jinjina kai ya ce "Allah ya bada sa'a, bani maganina" "Dan Allah ka daina shan magungunan nan, lafiyarka fa" Ya ce "Duba na na menene?" Ta ciro maganin ta duba, cikin magungunan sa ne na Asibiti, ta ajiye masa ta ce "Allah ya baka lafiya mai amfani, ya bamu nasara a kotu, in sha Allah case ɗin ka ne next, ka yi mana addu'a" ya jinjina mata kai. Ta tashi ta ɗauki jakarta tana ɗaga masa hannu. *** Daren yau Nabila tayi ta addu'a, suka yi waya da Barrister Habib, ya ce su haɗu a kotu. Ya ƙara mata ƙarfin gwiwa, kafin shiga shari'a, suna tsaye a harabar kotu, tana dudduba abun da zata tsaya a gaban shari'a da shi. Nabila ta tsaya a gaban kotu, ta ce my lord, kamar yadda na gabatar da hujjojina a wancan zaman da aka yi, akwai voice na  muryar mahaifiyar ramma tana kokawa akan a nema mata hakkin 'yar ta. Haryanzu ina da ja, a kan zargin da ake yi wa wanda nake karewa, a hirar da aka yi da mahaifiyar ramma, a gidan rediyo, wanda suka yi iƙirarin ya yi wa ramma fyaɗe, ya sha banban da wanda aka gabatarwa kotu. Haka zalika, voice message ɗin da yake yawo, na mahaifiyar ramma, ta koka a kan wanda ya yi wa ƴar ta fyaɗe, ya dawo ya ɗauketa ta ƙarfin tsiya daga gabanta. Lauyan gwamanti yayi suka, ya nemi da a gabatar da mahaifiyar ramma, ba wai kame-kame da abun da babu wanda ya san tushen sa ba. Nabila nan take ita ma ta buƙaci, a gabatar da ramma, tayi mata tambayoyi. Lawyan gwamnati ya ce Ramma na ƙarƙashin kulawar, likitoci haryanzu, dan haka ba za a gabatar da ita a gaban kotu ba. Nabila ta sake cewa Wane irin illa aka yi mata, da har zuwa wannan lokacin za ace ba ta warke ba, a shekarun baya shekara sha uku sha huɗu ake yi wa mata aure, ba a samun matsala, suna zaune lafiya, a report ɗin da aka bayar na case ɗin ramma, abun bai zama complicated da za ace tsawon wannan lokaci tana Asibiti ba. Lauyan gwamanti ya soki maganar Nabila, tare da neman a bashi dama ya gabatar da shaidunsa na gaba. Wata mata ce ta fito, aka tambayi baba mai gadi, ko ya santa? Ya ce Eh, ita ma mai aiki ce a gidan. Aka tambayi me ta sani, a game da abun da ake tuhumar mai gadi da shi, babu kunya babu tsoron Allah, ta bayar da shaidar zir, tare da tabattar da mai gadi ne yayi laifin, sai bayan da yayi aika-aikar, ta dawo daga sayen kayan miya, ta tarar da ramma, kuma daga shi sai ramma ta bari a gidan. Baba mai gadi ya sunkuyar da kai cikin matsanancin ɓacin rai da mamaki. Nabila ta ce ya za ayi ace gida kamar wannan babu cctv camera, akwai buƙatar idan da cctv camera a duba abun da ya faru. Daga nan Nabila ta nemi a bata damar ta gabatar da nata shaidar ma, aka bata dama, ta buƙaci wata mata ta fito. Nabila ta buƙaci matar ta gabatar da kanta, ta gabatar da kanta a matsayin maƙwabciyar su ramma a can garinsu. "Me ki ka sani game da abun da ya faru da ramma?" "Eh to, bayan an dawo da ramma gida, ta cigaba da jinya, dan sallamo su aka yi daga Asibitin birni, saboda rashin isashshen kuɗi. Babar ramma ta gaya mini wata mata ta zo ta ce zata taimaka musu, amma sai sun yarda sun janye shari'ar. Da suka ƙi, ta ce zasu gani, bayan wasu 'yan kwanaki, wani mutum ya zo da shi da wasu, ya gaya mata shi ne ya yi wa ramma fyaɗe, kuma ta ƙarfin tsiya, ya kama hannunta ya tafi da ita" Nabila ta ce "Ko ta gaya miki sunan wanda ya keta wa yar ta haddi?" "A'a, ba su san sunansa ba, ramma ba ta daɗe da fara aiki a gidan ba, amma ta tabbatar da ƙanin matar gidan ne. Bayan ya sace mata 'ya, ta je birni gidajen radiyo ba a saurareta ba, haka zalika wurin jami'an tsaro, kawai lokaci ɗaya muka nemeta muka rasa". "My lord, shaida ta tabbatar da cewa wanda ya yi wa ramma fyaɗe, ya dawo ya saceta, wanda nake karewa da ake zargi yake tsare, tayaya zai je ya sace yarinyar. Kuma har zuwa wannan lokacin, ba mu ga ramma a zaman kotu ba, shin ina ramma take?" Lauyan gwamanti ya ce bai kamata a karɓi shaidar maƙwabciyar su ramma ba, tun da ba a kanta abun ya faru ba, dan haka ayi fatali da shaidarta. Duk yadda Nabila ta so bayyanar da nagartar hujjojinta, amma kotu ta din ga soke su. Nabila tana ji tana gani, aka yankewa dattijon shekara goma sha huɗu a gidan yari, wata irin bahaguwar shari'a, mara fasali balle ɗigon adalci, yanke hukunci cikin gaggawa ba tare da kammala tabattar da ingancin shaidun kowane ɓangare ba, sai dai an basu damar ɗaukaka ƙara. Yanayin yadda ta fito a gigice kawai zai tabattar wa da mutum ba a hayyacinta take ba, sumayya da suka zo ɗaukan report ce ta nufeta da sauri, watsi ta yi da file ɗin hannunta, ta faɗa jikin sumayya tana kuka. Barrister Habib ya ƙaraso, ya ce "Haba Nabila, wannan ai sai ki saka ayi mana dariya, akwai appeal a gaba, dan Allah ki nutsu. Cikin kuka ta ce "Sumayya mu tafi gida, ba zan iya sake haɗa ido da mutumin nan ba, i try my best, ai kun ga yanayin shari'ar da aka yi, dama haka aka koyar da mu, an bi Principles na law a wannan shari'ar?" Sumayya ta din ga rarrashinta, suka sakata a mota, barrister Habib ya ce "Bari mu kaita gida, Bashir kai ka tafi da motata" Suna tafe a mota tana cigaba da kuka, Barrister Kabir ya kira Habib, ya ce "Ya ake ciki ne?" "Gamu zamu tafi, ba ta yi wining ba, sai kuka take yi" Kabir ya ce "Ai dama na gaya mata, waye ya gaya mata jayayya da mutanen nan abu ne mai sauƙi?" "Dan Allah kar ka saka ta sare gaba ɗaya, za mu yi appeal, kuma saboda ita nima zan yi abun nan kyauta fisabilillahi i really appreciate what she did" ya ajiye wayar yana cigaba da yi wa Nabila nasiha. Bunkure ta ƙyaƙyace bayan kammala wayar da ta yi, ta kalli badi'a. Badi'a ta ce "An kammala komai kenan?" "Eh, an ƙarƙare shari'ar a yau, uba ya yi abun da ya dace, wallahi da bai yi wani yinƙuri ba, sakar musu zan yi su ƙarata daga shi har ɗan nasa, su ta shafa, amma a wannan karon dole na ɗauki mataki a kan yarinyar nan, da gaske so take yi sai ta tona mini asiri, dole zan tattauna da indabo, ya ɗauki mataki a kan ta" "Amma kina ganin hakan zai yiwu, tun da abu ya shiga social media, kuma ta fara samun masu mara mata baya?" "Iyayen gidanta ma, ba su kai ko ina ba, amma an ce mini an hangeta da barrister Habib, kuma ina kyautata zaton da saka hannunsa a wani abun da take yi, amma duk na san matakin da zan ɗauka akan dukkansu" ta ƙarasa maganar tana haɗiye ƙwayoyin da suke hannun ta, ta bi su da ruwa. Nabila bayan sun kaita gida kuwa, ba ƙaramin kuka tayi ba, gaba ɗaya sai ta ji ta karaya, komai ya fita daga kanta. A ɗakin Nasir, ya sameta bayan ya dawo daga aiki, ko da ya tarar da Nabila ta sha uban kuka, tuntsirwa yayi da dariya, ya ce "Haba barrister, ina ƙwarin gwiwar ta ki? Har kin karaya haka?. Abun da na yi ta nuna miki kenan, nake gargaɗinki a kan ki fita daga sabgar nan, ba ke kaɗaice mai gaskiya a ƙasar nan ba, amma tun da ki ka ga kowa ya ja baki yayi shiru, to abun ya gagari kundila, amma ki ka ƙi ganewa ki ka cigaba da dagewa, ki gode Allah da ba su yi wani abu da za su taɓa lafiyarki ba ma" ya gama surutansa ya fita, ba ta ko kalleshi ba. Yana fita ta mayar da ƙofa ta rufe, tana ƙoƙarin kiran Viper, wayar Alhaji wada ta shigo. Ajiye wayar tayi, ta ɗauki ƙaramar ta ta, ta kira Viper. Bugu ɗaya ya ɗaga, kawai ta saka masa kuka. "Meye ne?" "Kana kallon wulaƙancin da aka yi mini a shari'ar nan, kaga wata irin shari'a da aka yi mai cike da wulaƙanci da zalunci, wallahi gaba ɗaya na karaya, na gaji da aikin nan, ina ji ina gani, mutumin da bai ji ba bai gani ba, zai tafi prison, zuciyata kamar ta fashe na gaji". "To ni kuma wa zai tsaya wa tawa shari'ar?" Nabila ta ce "I give up, na karaya" tayi maganar tana kuka. "Ke kin isa? Ai tun da muka fara, sai mun kai ƙarshe, tied your belt against next trial". "Ni ba zan iya ba, ina ga ma ciwon zuciya ya kama ni, duk na tsani komai, haka zamu cigaba da tafiya, mai kuɗi ne kawai ɗan gata? Ƙiri-ƙiri fa aka murɗe komai". "Sai ki gyara, kar ki gaji, sai kin gama da ni tukuna, anyway an hukunta wanda ya aikata laifin, saura kuma ki matsa ki gano in da ramma take da mahaifiyarta" "Wai kai wane irin mutum ne? Na gaya maka dattijon nan ba shi yayi laifin nan ba, kuma ni ina zan ganta?" Ko a jikinsa ya ce "Wannan matsalar ki ce ai, ki ƙarasa wannan ki zo ki yi nawa" Katse wayar ta yi, ta ajiye ta cigaba da kuka. ***** "Lakwari, ka je ka samu P.A ɗin Indabo, ka gaya masa ni na aikoka, ya uzzura mini da kiran waya, a kan lallai sai na je, wai mai zamani ya yi masa aike, dan haka dolena na nemo masa shi, haryanzu ban sanar masa da halin da nake ciki ba, amma ka je, idan ka je wurin P.A ɗin, ka kira ni zam yi masa bayani". "Shikenan, amma kana ganin ba za a samu matsala ba?" "Ba za a samu ba, daga nan ma sai ka samo mana kuɗin zuwa asibitin nan, dan na tattara kuɗin hannuna gaba ɗaya na aika a kawo mana ganye, shi ma kuma na ji shiru, idan ka dawo daga wurinsa ka biya ka duba mana". "Shikenan an gama" *** Nabila kuwa ba a iya Nasir ba, hatta yan gidan suka sakata a gaba da tsokana, suna yi mata dariya, bisa yadda ta shiga matsananciyar damuwar rashin nasarar da ta yi, a kotu. Ba ta taɓa yin shari'ar da ta shiga ranta ba kamar wannan, gashi dai kyauta take shari'ar babu ko sisi, amma duk ta bi ta damu, hatta hawa social media ya gagareta, saboda yadda ake yi mata dariya, ƴan koren Bunkure ke cigaba da nuna cewar Nabila hassada take yi wa bunkure, kuma kwangila ta karɓo a hannun wasu. Sosai ta fusata, ta hau social media tayi posting, ja da baya ga zaki ba tsoro bane ba, shirin faɗa ne. Kuma ko bayan shekara dubu, sunan gaskiya baya taɓa canzawa, a saurari fitowa ta gaba. Ɓangaren Nasir ma, yana fuskantar matsin lamba sosai daga wurin Indabo, da kuma manyansa a wurin aiki, a kan kama Viper. Gefe guda ga fargabar abin da Nabila za ta janyo musu, tun da ita ba ta so a zauna lafiya, yana matuƙar fargabar Indabo ya yi mata wani abun. Gaba ɗaya ta daina walwala, ko fitowa ta daina yi, sai idan fita zata yi, sai dai a kai mata abinci ɗaki a ajiye. Ganin ta takura kanta da yawa, Nasir ya sameta yana rarrashinta, da bata baki a kan ta jure ta karɓi ƙaddara. "Ba wata ƙaddara da zan karɓa" tayi maganar tana hura hanci. "Ke saɓo zaki yi kenan?" Nabila ta ce "DSP, abun da Allah ya hukunta shi ne ƙaddara, ba abun da mutum ya ga dama yayi da son rai ko son zuciya ba, ko da me matar nan take yawo, sai na tona mata asiri wallahi, gara ma ka ƙyale ni da wannan nasihar" "Na ƙyale ki, amma idan kin ƙi ji, ai ba kya ƙi gani ba, tun gashi yanzu kin fara ganin ma, amma ba wannan ba, wai haryanzu babu wani news da ki ka samo a kan Viper ne? Na ga duk kin yi sanyi, kin daina taimaka mini" Ta kalleshi ta ce "Ba dole na yi sanyi ba, ai dama ka ce na daina saka kaina a abun da babu ruwana, dan haka wannan ma babu ruwana da shi" Yayi murmushi ya ce "Haryanzu a fusace ki ke arfa, to ba ni ne dai Naja'atu Bunkure nan ba, amma yakamata idan da wani hints a taimaka mini" Ta kalleshi ta ce "Babu wani hints, ban san komai ba" "To shikenan, idan kin huce sai mu cigaba da maganar" ta harare bayansa har ya fice. Kasa samun nutsuwa ta yi, ta sake ɗaukar wayarta ta yi posting, "Idan har mahaifiyar ramma ba ɓata tayi ba, kuma da gaske Bunkure foundation na kula da ramma ne, to tana ina, al'umma yakamata su samu update a kan halin da take ciki, kuma shin suna da masaniya a kan ɓatan mahaifiyarta? Idan eh to ina tafi? Tana tare da 'yarta ne ko kuwa?" Tayi posting ta nemi wuri ta zauna, lissafi da tunani daban-daban suka din ga kaiwa suna komowa a cikin ƙwaƙwalwar Nabila. *** "Indabo, yakamata fa ka sake matsa Abdul, ya gaya maka in da yarinyar nan take, hankali ya fara dawowa kanmu, yarinyar nan fa ta matsa, kuma ban ga alamar, zaka ɗauki wani muhimmin mataki a kan ta ba" "Ya ce mini ya kasheta" Bunkure ta ce "Ya kashe ta ta yaya? A binciken da na yi, an tabattar mini uwar yarinyar ba ta garin nan, tafiya ta yi babu shiri, kuma Abdul ya je gidan fiye da sau ɗaya, bayan ya ɗauke yarinyar, me ya je yi, ni fa ba na son a din ga gaba ana baya, kar asirinmu ya tonu fa" Indabo ya numfasa ya ce "Abubuwa sun fara caza mini kai Naja, ga takarar Abdul da nake ta fafutuka, ga auren nan da ake shirin yi na shi. Ga ɓangaren ki taki matsalar, duk is a minus case, bababr damuwata yanzu Viper, aiken da ya yi mini ya tayar mini da hankali, idan ba a kama shi an kashe ba, hankalina ba zai taɓa kwanciya ba, ga ƴan adawa sun sako mu a gaba, ga tunanin jafar da yake tsare na rasa wane tunanin ma yakamata na yi" "Ai wanda ya fi muhimmanci shi zaka yi, wallahi idan aka cigaba da ƙyale yarinyar nan, muna raina abun da take yi zata bamu mamaki fa" Ya jinjina kai ya ce "Na ga alama, kuma ba zan taɓa bari hakan ta faru ba". P.A ne ya kaste su, ta hanyar yin sallama, suka amsa duk suka ɗago suna kallonsa. Ya kalli indabo ya ce "Akwai matsala fa" "Again?" "Ƙwarai kuwa, madaki ne ya yi aike, wai ya samu rauni a ƙafarsa, yanzu haka ko iya tafiya ba ya yi, ɗazu ya turo yaronsa har ya buƙaci a bashi kuɗi ya je asibiti, amma wai duk wani abu da yakamata, yana da yaran da za su iya yi maka" Indabo ya buga tsaki ya ce "Maganar banza kenan, zuwa yaushe zan cigaba da rarraba sirrina, wannan yayi mini aiki wancan yayi mini, kalli yadda haryanzu jarabar ɗan tahaliki ɗaya take ta ɗawainiya da rayuwata. Na gaji ya je Allah ya kyauta, na nemi wata mafutar" "Amma kana ganin watsi da shi, ba zai zame mana wata ɓarakar ba ko barazanar ba?" "Babu abun da zai zame mana sai wahala, tun da ba shi da wani amfani yanzu, Viper da na bari ya ci karensa babu babbaka, saboda yaron dodo ne, ina matuƙar jin tsoron abun da ya sani a kaina, kuma kamar yadda na yi tsammani, ya san abubuwan da idan yayi magana kashinmu ya bushe, dole fa a nemo Viper akwai matsala wallahi" yayi maganar yana zazzaro ido cikin tashin hankali. Sai da aka kusa sati da yanke hukunci, sannan Nabila ta tafi wurin iyalan dattijon nan, tare da sake rarrashin su, a kan su yi haƙuri su ƙara mata lokaci, zata ƙara shiryawa sosai a appeal ɗin da za su yi, tana saka ran za su yi nasara in sha Allah. Suka yi ta yi mata godiya, sai da zata tafi, ƙaninsa ya keɓe da ita, ya ƙara yi mata godiya, sannan ya ce "Dan Allah ki ƙara bincikar ɗan uwana, kamar fa ya san wanda ya yi laifin, barazana aka yi masa Shiyasa ya kasa gaya miki komai" "Barazana kuma, wace irin barazana?" Ya ce "Eh, akwai ziyara da na kai masa, ya gaya mini amma ya nemi kar na gaya wa kowa, ya san sunan wanda yayi laifin, da alaƙarsa da matar gidan, amma bai san ɗan waye ba" Ta ce "Ya salam, to amma meyasa ni bai gaya mini ba, babu yadda ban yi da shi ba a kan idan ya san wani abu, ya sanar mini, amma ya ce mini babu abun da ya sani, sunansa ma bai sani ba, kawai dai ya san ɗan yayan matar gidan ne". Ta ce "Subhanallah, shikenan zan san abun yi, a cigaba da yi mana addu'a" Ya ce "In sha Allah, kullum cikin yi muku ake, Allah ya jiƙan magabata mun gode sosai da sosai". Tana kan hanya saƙon Viper ya shiga wayarta, a kan yana son su haɗu. Ji tayi kamar ta maze taƙi zuwa, amma ina, ba ta ji alamar zuciyarta zata bari ta aikata hakan ba. Garden ɗin da suke haɗuwa, a can ta same shi, ta tsaya tana kallonsa ya rage sumar kansa, yayi kyau sosai. Wata tab ta gani a hannunsa, cikin basarwa ta ce "Ina wuni?" "Wayarki zaki bani" Ta kalleshi ta ce "Wai baka san meya same ni bane? Baka jajanta mini rashin nasara da nayi ba, abu duk ya dame ni" "Yanzu ki ka fara, idan har rashin nasara ba zai saka ki ƙara jajircewa ba, sai dai ki yi kuka" Nabila ta ce "To idan ban yi kuka ba ya zan yi?" Ya kalleta ya ce "Babu" "Waye ya sai maka waya?" Yayi mata shiru. Ta sake cewa "Haryanzu fa ina da tarin tambayoyin da baka amsa mini ba" "Wanne daga ciki?" "Meyasa Indabo ya ce zai yi maka tarko da ni ya kama ka? Ni meye haɗina da kai?" Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Wataƙila ya san kina zuwa wurina" "To amma ya aka yi haryanzu bai kama ka ɗin ba? Kuma ni haryanzu kana ɓoye mini wasu abubuwa" Ya saka ƙaramar wayarsa a kunnensa, ya ce "Ɗan mama ya ake ciki?" "Oga Viper, mun ƙwamuso Lakwari fa, yanzu duk in da madaki yake, dole ya bayyana, tun da babu mai taimaka masa ko ya kula da shi" Viper ya ce "Good job, zan gaya muku what next" Cikin zaro ido Nabila ta ce "Viper kidnapping?" "Eh ina son na sauƙaƙa miki aiki ne, shaidu na fara tattara miki, kafin a fara shari'ata, Madaki yayi jigatar da ba zai iya musa laifin da ya aikata ba" "Amma ka gaya mini me ka ke yi da wayoyi? Ka daina yi mini ɓoye-ɓoye. Sai kin zo kan shari'ata zaki ji koma me ki ke buƙatar ji" Kamar shashasha haka take kallonsa, gaba ɗaya ta ma rasa me za ta ce masa. Ya miƙa mata wayarta ya ce "Angry bird" "Am confused" "Sorry" Kamar ta sake fashewa da kuka ta ce "Zuciyata kamar a kurku, haka nake jin ta, mai laifi daban yana can yana rayuwarsa, mai karɓar hukunci daban, wane irin abu ne wannan?" Viper ya gyaɗa kai ya ce "Kamar dai ni a kwanakin baya, idan aka kama mai laifi, sai ayi musanye a saki wancan saboda ɗan gata ne, ni kuma a tsare ni a matsayin mai laifin" Ta ce "Kuma dai? Wani yayi laifi kai kuma a tsareka?" "Mmm, a saka matata tayi ta yawo tana wahala ba, wata Shari'a sai a lahira, duk rintsi kar ki yadda ayi amfani da ke ki ci amana, ba kowa ne yake da zuciyar yafiya ba" Jiki a sanyaye ta jinjina kai, ya ce "You can leave". Kusan a tsukin lokacin, Nabila ta zama topic of discussion a social media, sai dai ba ta karaya ba, wurin cigaba da posting a kan bunkure foundation. *** "Abdul tun muna shaida juna, ka gaya mini ina yarinyar nan take? Ka kashetan ko kuwa? Sannan uban me ya sake mayar da kai gidansu, bayan ka je ka ɗauki yarinyar, kuma saboda hauka maimakon ka saka ayi? Kawai sai ka wanke ƙafa ka tafi da kanka ka je ka ɗauki yarinyar, kamar baka san matsayinka ba? Idan ka san uwar yarinyar nan ma, tana tare da kai, ka gaya mini, na san matakin da zan ɗauka a kai" Ya girgiza kai ya ce "Ni ban ɗauki uwar yarinyar ba, ban san in da take ba" "Da ka kashe yarinyar yaya ka yi da gawarta?" Abdul ya ɗan yi jimm sannan ya ce "Ruwa na jefa ta" Indabo ya ja guntun tsaki ya tashi, maganganun da bokansa ya gaya masa ne suke ta yi masa kai komo a zuciyarsa, wai dutsen da ya gaya masa zai ci karo da shi, lokaci yayi da shi bai san ya za ayi ba, dole ayi ɗayan biyu, ko dutsen yayi nasara a kansa, ko kuma su yi mutuwar kasko, amma babu yadda za ayi, ya iya maganin dutsen nan da kansa. Nabila fa ta sake jajircewa, da cigaba da ƙoƙarin gano bakin zaren matsalolin da take tunkara. Bayan shari'ar ramma, akwai shari'oi da dama a gabanta, amma wannan c ta fi ci mata tuwo a ƙwarya, sai kuma ta Viper da zata fuskanta. Kasancewar da sassafe ta je wurin aikin, duk babu mutane, ta shiga office ɗin ta, ta ajiye jakarta, ta yi addu'a ta zauna, ta buɗe computer ta fara aiki. Ƙaurin wayar wutar lantarki ta fara ji, ta ɗaga kanta, ba ta ga komai ba, ta sunkuyar ta cigaba da aikinta. Wata irin ƙara wearing ɗin office ɗin ta yayi, ya fara ci da wuta, a razane ta tashi cikin tashin hankali, ta nufi ƙofa zata buɗe, ta ji an kulleta ta waje, ta jijjiga iya ƙarfin ta, amma a ƙofar a kulle gam, ga wuyar wuta sai cigaba da ƙara take yi wuta na kamawa tana tarwatsi. Da ƙyar ta iya ɗaukko jakarta, ta ciro wayarta, tuni ta fara gani dishi-dishi, saboda hayaƙi, tari ya turnuƙeta. Hannunta na rawa, lambar Viper kawai ta iya gani, ta danna. Ya ɗaga wayar sautin tarinta ya fara ji, tana ta yi haɗe da haki, da ƙyar ya iya fahimtar ta ce "Wuta" daga nan ya ji ɗif Ayshercool 08081012143 64 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin hanzari Viper ya tashi ya tsaye, yana cewa "Kina ina ne? Meyake faruwa?" Sai dai still shiru ba ta ce komai ba. Su Walid ma duk suka miƙe tsaye, suna kallonsa. Walid ya ce "Yaya meyafaru Viper?" "Ki yi mini magana, kina ina meyake faruwa ne?" Liti ya ce "Mai zamani menene wai?" "Yarinyar nan tana cikin matsala" "Subhanallah, to tana ina ne yanzu?" liti yayi maganar yana kallon sa. "Safiya ce yanzu, ko tana gida, ko hanya ko wurin aiki. Babu yadda za a yi ace a gida ne wani abu ya same ta ta kira ni, da hanya ne kuma da tuni an kai mata ɗauki, ko dai an ɗauketa ne ko kuma tana wurin aiki, wuta na ji ta ce" Hanyar fita Viper ya nufa, Walid ya riƙe shi ya ce "Ina zaka fita ka je? Ba kai yakamata ka fita ba, liti ko ɗan mama, ɗan maman ma dai, ka san wurin aikinta ai in da kuka ɗaukkota?" Ya ce "Eh oga Walid" "Je ka gano mana menene yake faruwa" Ya ce "To bari na canza kaya" Viper ya cigaba da bin layin Nabila yana kira, amma shiru ba ta ɗagawa. Nabila kuwa tuni ta fice daga hayyacinta, ba ta sake sanin in da kanta yake ba. Masinja ne da shigowarsa kenan, ya ga wurin ya turnuƙe da hayaƙi, ya shiga dudduba daga ina hayaƙin yake fitowa. Cikin tsananin tashin hankali, ya nufi ƙofar office ɗin Nabila, ya din ga bubbuga ƙofar, amma ya ji ta a rufe gam, ya girgiza ya girgiza amma a rufe, ya fito ya nufi wurin masu gadi, ya na sanar da su wuta. Suka tashi gaba ɗaya suka rankaya a guje, ɗaya daga cikin su ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Nabila fa ta shigo aiki, tana ciki jama'a ku taimaka". Nan da nan wuri ya cika da mutane, ana ta ƙoƙarin a ɓalle ƙofar a cirota, a daidai lokacin barrister Habib ya ƙaraso cikin tashin hankali, kasancewar an kira shi a waya an sanar masa. Da kyar aka ɓalle ƙofar, wani irin huci mai ɗauke da hayaƙi ya buso waje suka ja da baya, wani matashi ne ya kutsa kai, ya na nemanta, ya hangota a yashe a cikin office ɗin ga jakarta da system ɗin ta, da wayarta a wurin. Wutar ta mutu ba ta cigaba da ci ba, iya wadda ta kama ce ta haddasa hayaƙi, da huci mai zafi. A kafaɗarsa ya saɓo Nabila, yana fitowa barrister Habib ya karɓi wayar da system ɗin, yayi waje da ita. A motar barrister Habib aka saka ta, suka nufi asibiti. Barrister Kabir ma hankalin sa yayi mummunan tashi, ya din ga kiran waya, Habib ya ce masa sun tafi da ita Asibiti. Gaba ɗaya hankalin ma'aikatan wurin ya tashi, dan duk jin kan Nabila da gayunta akwai girmama mutane, ga yawan kyauta da take yi musu. Viper ya kasa zaune ya kasa tsaye, Liti da Walid ne suke ta rarrashin sa, amma ya kasa nutsuwa, sai cewa yake tafiya zai yi ya gano halin da take ciki, suka din ga kiran wayar ɗan mama, amma bai ɗaga ba. Viper ya ce "Walid, ba zan lamunci a wannan karon wannan ita ma ta rasa ranta ba, dole fa na gano halin da take ciki" Walid ya ce "Mun sani, amma ka fara bari mu ji daga bakin ɗan mama" Suna tsaka da maganar ya kira waya, Viper ya fizge wayar daga hannun liti, ya ɗaga ya ce "Kai ana ta kiranka ka ƙi ɗagawa, yaya aka yi ka sameta?" "Wuta ce ta kama fa a ofishin ta, lokacin da na je an buɗe ƙofar an fito da ita, za a tafi asibiti" "Dalla ba wannan na tambayeka ba, tana ina yanzu a wane hali take ciki?" "Eh, sun tafi kaita Asibiti, na bi bayansu a adaidaita sahu, an kaita wani ɗaki an hana kowa shiga, haryanzu dai ina asibitin, likitocin dai ba su ce komai ba, amma dai kamar fa ba ta da rai" Ashar Viper yayi masa, ya ce "Yaya aka yi ma wuta ta kama a iya  ofishin ta kawai? Me hakan yake nufi? Likitoci sun ce ta mutun ne?" Ɗan mama ya ce "A'a ni nake tunanin hakan, bata motsi ko numfashi a yadda naga an sakata a mota wallahi da ƙyar idan ba mutuwa za ta yi ba" Liti ya ce "Ɗan mama ko ɗan shegiya, gaba ɗaya yaron nan gaɓo ne, ya za ayi ka gaya masa wannan maganar?" Walid ya karɓi wayar daga hannun Viper, ya saka a kunnensa ya ce "Ɗan mama kana ji na?" "Eh oga Walid" "Duk abun da ka ke ciki, ka din ga sanar da mu" "To oga walid in sha Allah" "Jikinta wutar ta taɓa ta ne?" "A'a, ba ta ƙone ba, hayaƙi ne ya yi mata illa, wutar ma ba ta kama sosai ba" "To shikenan, muna saurarenka" Walid ya kalli idon Viper, yadda ya bayyanar da matsanancin tashin hankali. "Viper, ka kwantar da hankalinka dan Allah komai zai zo da sauƙi, in sha Allah ba zata mutu ba, sai ta cika maka burinka" Jiki a sanyaye ya ce "Walid yanzu shikenan duk wanda ya raɓe ni, rayuwarsa sai ta shiga hatsari, idan ita ma ta rasa ranta fa, jikina yana bani set up ne abun nan" Liti ya ce "Kar ka zargi kanka, dama can wannan ba ta ji, kuma haryanzu ai bata fara shari'ar ka ba, balle ace saboda kai ne" Walid ya ce "Ya isa haka liti, kai abu ba ya wucewa a wurinka" "Yaushe zai wuce, tun da ta munafurce ni, ta saka aka kamani" *** Abba kuwa Allah ne ya tsare bai yanke jiki ya faɗi na, bayan sanar masa da cewar, gobara ta kama a ofishin Nabila tana Asibiti. Haka Nasir ma, cikin gigita da tashin hankali, ya nufi Asibitin da aka ce an kai Nabila. Likitoci sun hana kowa ya shiga, an cire mata kaya an saka mata wata gown, ana duba jikinta ko da in da ta ƙone, amma babu, sai dai ga zuciyarta na bugawa, amma babu numfashi, idan tayi kamar zata yi numfashi, sai tayi ta tari, hayaƙi na fita ta hancinta da bakinta, sai tayi ɗif. Gaba ɗaya Abba a rikice ya ƙaraso asibitin, cikin matsanancin tashin hankali Abba ya ƙarasa asibitin, zuwansa babu daɗewa Nasir ma ya ƙaraso, Abba ya nemi a bar shi ya ganta, amma aka ce ba a shiga likitoci na aiki tukuna. Abba ya ce " 'ya ta ce, ko me za ayi mata ayi a gabana, idan ma ta mutu ne a bari na ganta, ai ni musulmi ne na kuma yadda da ƙaddara mai kyau ko mara kyau" suna ƙoƙarin lallaɓa shi ya haƙura kar ya shiga, ya burkice musu, babu shiri aka bashi damar shiga wurinta. A kwance ya tarar da ita, ana ta allurai, ya ƙarasa gaban gadon ta ya zuba mata ido, dama ya lafiyar kura balle ta yi hauka, an sha wahalar ciwonta na asma sosai da sosai, sai da ta girma ta ɗan samu sassauci, tayi gado mai wahala, dan mahaifiyarta ce mai ɗauke da ciwon ta gada. Ya kalleta a kan gado, sai ya ga ta koma masa kamannin mahaifiyarta sosai da sosai, lokacin da take gadon asibiti ta riƙe hannunsa a halin rashin lafiya. Ya riƙe hannun Nabila, ya ga alamar akwai rai a jikinta, amma a galabaice take, ya daɗe yana yi mata addu'a, sannan ya tashi ya fita waje. Barrister Kabir kuwa tuni suka yi reporting wurin Jami'an tsaro, aka zo aka fara bincike a kan musababbin tashin wutar, abun bai tsaya iya nan ba, sai da aka tattare masu gadin wurin, aka tafi da su wurin 'yan sanda domin fuskantar tuhuma. Sumayya ma tun kan ta ƙaraso asibitin take uban kuka, saboda yadda aka gaya mata faruwar abun, ta riga ta fitar da rai Nabila tana raye. Sai da Nabila ta shafe awa biyu, likitoci na procedure daban-daban a kanta, aka samu numfashinta ya dawo, sai dai a wahale take yin sa, aka fito da ita daga emergency, aka mayar da ita wani ɗakin. **** Bunkure ta daki tebur ta ce "Tana raye kenan?" Mutumin gabanta ya ce "Eh ranki ya daɗe, an samu nasarar fitar da ita daga wurin, amma na samu tabbacin tana raye, bata mutu ba sai dai tana cikin mawuyacin hali" "Babu ruwana da mawuyacin hali, wannan wane irin aiki ne? Yaya za ayi ni ga yadda muka yi da ku, amma abun da ku ka yi daban?" "Ba daga mu bane ba ranki ya daɗe, wallahi aiki an yi shi yadda yakamata, agajin gaggawa aka kai mata shiyasa" Ta numfasa ta ce "Shikenan, zaka iya tafiya, a asibitin zan saka a ƙarasata". *** Hankalin Viper bai dawo jikinsa ba, sai da ɗan mama ya dawo, ya tabattar masa da a kan idonsa aka fito da ita, tana raye, kuma ba ta ƙone ba, ko ƙwarzane babu a jikinta. Nannauyar ajiyar zuciya Viper ya sauke, yana fatan Allah ya sa hakan, ya kuma bata lafiya. Hatta 'yan gidan su Nabila, sai da suka tausayawa halin da take ciki, duk da ba shiri suke yi da ita ba, baba magajiya kuwa kuka ta ɗora hannu a ka ta din ga yi, ba ta san iya tashin hankalin da zata shiga ba, idan aka ce ba Nabila. Sumayya na gefen Nabilan, ta riƙe hannunta tana ta matsar hawaye, tari ne ya kuma turnuƙe ta, kawai ta yinƙura zata tashi zaune, duk suka nufo kanta, Sumayya ta riƙeta tana kiran sunanta. "Viper wuta, wani ya kulle ni ta waje, ku taimaka mini, Viper wuta" gaba ɗaya sai suka yi sak, suka zuba mata ido. Abba ya ce "Waye kuma Viper?" Cikin matsananciyar tuhuma Nasir yake bin ta da kallo, da yake ta surutai cikin fita hayyaci. Barrister Habib ma sak yayi, Sumayya ta ce "Abba sunan wani ɗan daba ne, da take bincike a kan sa, maybe tana ƙadamin aiki a kansa ne abun ya faru" Abba ya ce "Na rasa irin Arfa, wataƙila ma a dalilin wannan kwashe-kwashen nata, aka yi yinƙurin cutar da ita. Barrister Habib ya ce "Bana tunanin haka sir, maybe ƙaddara ce kawai, ai tana yawan zancen ɗan daban nan ne, ta ce Yayanta shi ne incharge na nemansa tana fatan ta taimaka masa" Nasir duk da ido yake bin su da kallo, yanayin yadda take surutan, kamar akwai sabo da kuma shaƙuwa a tsakanin su. A hankali sumayya ta ce "Masoyiyya" "Na'am sumy" "Na'am" "Wuta aka saka mini a office ɗina, da ta tashi, na tafi da gudu na buɗe ƙofa na ji an rufe ni ta waje" Abba ya ce "A'a Arfa, Allah ne dai ya ƙaddara tashin wutar, kar ki zargi kowa" Nabila ta ce "Abba, ni fa na buɗe office ɗin da kaina, na bar key a jiki ta waje na shiga, da wutar ta tashi na je na buɗe, na ji an murɗa key ɗin sau biyu" Abba ya ce "Ki na cikin hayyacinki, kin farka gaba ɗaya?" Ta jinjina masa kai. Ya ce "Alhamdilillah" nan aka din ga jera mata sannu, duk da tana ta haki a hakan ma. *** Ramma ce a tsaye, ta shirya cikin doguwar rigar abaya, ta ɗora mayafin a kanta, Abdul ya bata facemask ya ce "Saka wannan" ta karɓa ta saka, ya ce "Wow, kin yi kyau sosai beb" ta yi murmushi tare da gyara mayafinta. Ya riƙe hannunta, har cikin motarsa, da hannu ɗaya yake tuƙi, hannunsa ɗaya kuma ya riƙe nata, loka-lokaci sai ya sumbaci hannunta, yana jin wani irin so da shauƙinta yana ratsa ilahirin jikinsa. "Ni ka daina shafa mini yawu a hannu" "Haba Rahama, yawun ƙauna ne fa" yayi maganar yana satar kallonta. Ta jingina da seat ɗin motar, ta numfasa ta ce "Yaushe ne bikinka, ko an yi ne?" Ya ce "A'a, ya za ai, ayi ba ki sani ba? Wai bata ƙarasa karatu ba, da an so ayi ne idan ta dawo shikenan ta tare, babanta ya ce a bari ta gama, saura 2months" Ramma ta ce "Allah sarki, ni nawa karatun ko oho, na zama karuwa" "Haba rahama, dan Allah ki daina wannan maganar, ina da kyakykyawan tanadi a kan rayuwar ki da iliminki, na san na cutar da ke, amma zan gyara laifina in sha Allah" tayi masa shiru tana kallon titi. Dare ne sosai, duk sahu ya ɗauke. Ya zuba mata ido, a lokacin da take shan ice cream ɗin gabanta, ya tuna yadda yake ta fama da mahaifinsa, ya tsunduma tunanin ya zai yi ya sanar da shi batun ramma? Dan sai dai ayi wadda za ayi a kan ramma, amma bai ji duk iya bala'in da za ayi zai rabu da ita ba, ta kalleshi ta ce "Ka sha mana" yayi murmushi ya jinjina mata kai, mama ya cigaba da jujjuya cokalin. Hakan ya sanya ta fuskanci a cikin damuwa yake, ta ɗebo icecream ɗin ta kai bakinsa, ya ɗaga ido ya kalleta, ya buɗe bakinsa ya karɓa. Ya ce "Kin yafe mini dukan da nayi miki, kin daina fushi da ni?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "To ɗaya laifin fa?" "Ban yafe wannan ba" ta bashi amsa kai tsaye. "Tun da ki ka yafe wannan, wancan ma zaki yafe mini in sha Allah" ta yi shiru tana kallonsa. Sai da ta gama ciye-ciyenta son ranta, sannan ya ce ta raka shi asibitin abokinsa, zai duba wasu marasa lafiya. A zuciyarsa yake zargin kamar wani cikin ne da ramma, amma bai tabattar ba, kuma bai ambata ba, balle ta tashi hankalinta, muddin kuma ya ce zai gwada za ta gane, kuma ta daina yarda da shi, dan ce mata yai, yayi mata allurar planing, ba zata sake ɗaukar ciki ba sai allurar ta sake ta. Waɗanda ya yi wa tiyata a asibitin ya duba, sun fito take tambayarsa "Nan ne asibitinka?" Ya ce "A'a, Asibitina na can wajen gari, na kan je wasu asibitocin da aka buƙace ni, na gabatar da aiki, zan kai ki namun ma ki gani" Ramma ta ce "Naka dai" "A'a namu dai, idan komai ya daidaita, ai bikinmu za ayi, na nuna wa duniya ke, komai ya wuce" Ta ce "Taɓ kwaɗo" Babu tsammani yayi karo da wata matashiyar budurwa, hannunta riƙe da ledar Pharmacy. "Ke ba kya gani ne?" "Ban gane bana gani ba, kawai ka zo ka tsaya a hanya, kana rangwaɗa, da alama kai jin daɗi ne ya kawo ka asibitin ba mara lafiya ne da kai ba" Ramma ji tayi kamar ta san muryar. A fusace ya yinƙura zai yi masifa, ramma ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri, mun tsare hanya kam, Allah ya ƙara afuwa ga mara lafiyan" Sumayya ta amsa da "Amin" ta harare shi ta wuce. "Dan Allah ka din ga rage faɗa, har marasa lafiyar ma, faɗa ka ke yi musu, haba kai kuwa" ƙwafa yayi suka tafi. *** Sosai Viper yake son kiran wayar Nabila, amma babu hali, dan ɗan mama ya tabattar masa da ya ga an fito da wayarta, da jakarta da system ɗin ta, wani mutum ya karɓa, amma alamu sun nuna a wurin yake aiki shi ma. Viper bai san waye ya karɓi wayar da system ɗin ba, akwai ayyukansa a cikin system ɗin ta, da suke buƙatar sirri sosai da sosai. Nasir ya karɓi system ɗin Nabila da wayoyinta a hannun barrister Habib, sai dai ya kasa buɗewa, dan bai san menene password ɗin ta ba, har su walida ya tambaya ko sun sani, suka ce ba su sani ba. Ƙaramar wayarta kawai ya iya buɗewa, sunan confidential ya fara nema, yayi sa'a ya samo lambar, sai dai ya duba lambar da aka yi saving a kan sunan, ya tarar da suna babu lamba, ya duba ya duba, amma ya rasa samun lambar, ya din ga kwafar lambobin wayar, yana dubawa a Truecaller ɗin sa, amma babu wani suspicious abu da ya samu. Yanzu tantamar da yake yi a kan Nabila, ya wuce zargi, akwai abun da take aikatawa na rashin gaskiya, ya ƙallafa ransa sai ya gano, waye wannan mutumin da ya gansu tare sau biyu. A kunne ya bar wayoyin, sai dai yadda aka din ga kira babu ƙaƙƙautawa, tun yana ɗagawa yana saka ran, zai samu wani abu na information, harya haƙura ya daina ɗagawa. Nabila ta farga da rashin wayoyinta, ta tambayi a bata wayoyinta, aka ce mata suna wurin Nasir, ta jira ya zo Asibitin ta ce ya kawo mata wayoyinta ya ce ba zai bayar ba. Cikin mamaki ta ce "Amma meysa na san za a neme ni a wayar?" Ya ce "Kina fama da kanki, uban me zaki yi da wata waya?" Sumayya ta ce "Ke ma dai arfa, uban meye a wayar ne, ki hutawa kanki ki gama farfaɗowa" kallon Nasir take yi, tana nazarin irin kallon da yake yi mata, ta fara fatan Allah ya sa ba wani abun ya gano a wayar ba. Abba ne ya shigo, suka gaggaisa, ya din ga tsokanar Sumayya tare da Nabila, ko wurin aiki Sumayya ba ta zuwa, tana liƙe a asibiti da Arfa, Sai da Nabila ta magantu a kan wurin aikin sumayya amma ta basar da ita. Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin aka yi, sannan aka buɗe. Jmau'an tsaro ne da bindigogi suka fara shigowa, gaba ɗaya suka yi ƙuri da ido, suna kallonsu. Alhaji wada m karofi ne ya shigo, suka gaisa da Abba, Nasir ma ya gaishe shi. Nabila ta ce masa "Lafiya, wannan kama ni za su yi?" Yayi murmushi ya ce "Saboda ke ce Sarkin laifi ba, yaya jiki ashe haka wannan iftila'in ya faru?" "To ai na ganka da yan sanda me na yi?" Yayi mata shiru, suka ƙarasa gaisawa da Abba suka gaisa, Sumayya ta ce "Ina kwana?" "Lafiya ƙalau T ladan, ya gidan radio?" "Yana nan sir" Nabila ta ce "Dama kin san shi?" Sumayya ta girgiza kai. Ya ce "Eh ba lallai ta sanni, amma ita muryarta sananniya ce ai, kuma kina bani labarinta ai, ko ba sumayya T ladan ba ce?" Sumayya ta jinjina kai tana murmushi. Nan yake gaya wa Abba, ai a law firm ɗin Barrister Kabir yake ganin Nabila suke gaisawa, shi yake sanar masa tsautsayin da ya faru. Nasir dai ya din ga mamakin yadda karakainar Nabila, ta kai ga ta ga sanin manyan mutane har haka, bayan ya gama duba ta, yayi musu sallama ya tafi, Nasir ma da Abba tafiyar suka yi, aka bar sauda da Sumayya, suna tafiya Saudan ma ta shura takalmanta ta fice, dama ba son zaman take yi ba. Sumayya ta kalli Nabila ta ce "Nabila na ajiye aikina fa" Nabila ta waro ido ta ce "What? Saboda me?" Sumayya ta numfasa ta ce "Hakan shi ne yafi dacewa ne" "Sumayya wannan ai wauta ce, meyasa zaki ajiye aikin?" "Na gaji da barazanar da ake yi mini, da tashin hankalin da ake yi mini, Allah ya taimake ni an shiga tsakanina da indabo, ya rabu da ni, amma support ɗin da muke baki, da ni da yaya murtala baki ga rashin mutuncin da ake yi mana ba, ga hantara da tsangwama. Da barazanar kora babu yau babu gobe, na ajiye musu bakin da Allah ya tsaga ba ya hana shi abun da zai ci" Cikin matsanancin damuwa Nabila ta ce "Sumayya baki kyauta mini ba, da ki ka ɓoye mini wannan babban al'amari haka, ki rasa aikinki a dalilina, haba sumayya". Sumayya ta yi dariya ta ce "Kar ki damu, umma ma ta sani, kuma ta bani ƙwarin gwiwa yaya murtala yana yi mana processing ɗin wani sabon gidan radio, za su bani aiki da ni da shi, shi ma baro can zai yi, su ci kansu" Cikin damuwa ta ce "Sumayya duk da haka ban ji daɗi ba, idan kuma ba a samu aikin ba fa?" "Zafa a samu in sha Allah, na bawa yaya murtala cv na, ya ce mini sun yi murna sosai da jin zan koma wurinsu, sabon gidan radio ne, za a buɗe dama lawisa a ƙule take da ni, ta ƙara takura mini, saboda mutane suna yi na, sai su kwaɗa gidan radion su cinye" Nabila ta numfasa ta ce "Sai mu duƙufa addu'a masoyiyya, Allah ya sa ki samu ya tabattar da dukkanin alkhairansa" "Amin, amma Nabila wannan wutar kuwa ba set up bane ba, ana sane aka sakata ba?" Nabila ta ce "Set up ne mana, sai da na shiga na zauna sannan ta kama, na taho na fita kuma, aka sakawa ƙofar key" "Wa ki ke zargi?" Ta girgiza kai ta ce "Bana zargin kowa, abun da nake yi ne dai ba zan bari ba" "Nabila" "Na'am sumayya T ladan" "Haryanzu kina zuwa in da Viper yake kuna haɗuwa?" Nabila ta kalleta ta ce "Wace irin tambaya ce wannan?" "Amsa zaki bani, ba ki tambaye ni ba" "Ban ga gurbin yin tambayar a nan ba, ko dai haryanzu yaudarata ki ke yi, aiki ki ke yi wa Indabo a kaina?" "Ko kaɗan, indabo ma Allah ya yi mini maganinsa, ya rabani da shi, amma alamu sun nuna kina haɗuwa da Viper, da sunansa ki ka farfaɗo a bakinki" "Tuhumata ki ke ko zargi?" "Babu ɗaya" "To idan har ba aiki ki ke yi wa wani a kaina haryanzu ba, to ki bar maganar nan" Sumayya ta ce "Shikenan, an bar ta" Likita ne ya shigo, ya kalli Nabila ya ce "Barrister jiki yayi kyau, jiya doctor yasar ya shigo, ai da na sani nayi masa magana ya duba jikin naki, idan da wani abu da zai ƙara miki" "Doctor ni dai dan Allah ka sallame ni, na gaji wallahi" "Ki yi haƙuri, zai sake shigowa yanzu, mun yi waya da shi, zai ga masu hawan jini kan ya wuce, kin san shi abun ne ya haɗar masa, ga siyasa ga kuma aikin likita" "Ashe kuwa zaka neme ni ka rasa a asibitin nan, tafiya ta zan yi na gaji" "No ba za ayi hakan ba, bari na rubuta miki sallama, Alhamdilillah ai jiki yayi kyau sosai". Sumayya ta ce "Mun gode sosai doctor" Tashin hankalin da Indabo yake ciki a yan kwanakin nan, duk sai tsufansa ya fito, ko bacci baya iya yi sai ya sha ƙwayoyi, saboda damuwa da tashin hankali. Cikin dare ya ga kiran Wada karofi, ransa ya ɓaci kamar kar ya ɗaga, sai kuma ya ɗaga ya ce "Karofi wani irin wulaƙanci ne ya sanya kake kirana ƙarfe ɗaya na dare?" "Kashedi, da kuma gargaɗi, Nabila ta tsallake wannan tarkon da kuka yi mata, kamar yadda na taka maka burki a kan ƙawarta, ina mai ja maka kunne a kanta, wallahi wani abu ya samu yarinyar nan, zan yi abun da baka so" "Wacece hakan?" "Ka fi ni sanin wa nake magana a kai indabo, mukiyaye abun da zai zubar mana da mutunci a idon duniya a matsayin mu na 'yan siyasa kuma sirikai da ni da kai, ba zan lamunci wani mummunan abu ya same ta ba, mu cigaba da yaƙar juna ta ƙarƙashin ƙasa kar duniya ta ji wannan labarin ka kiyaye" *** Madaki ne ya lallaɓo ya fito daga cikin ɗakin da yake, yana ta kiran wayar lakwari, amma taƙi shiga. Walid ya gani a tsaye, yana kallonsa, ya tsaya cak, suna kallon kallo. Walid ya yi murmushi ya ce "Duk ƙoƙarin da ka yi, ka gaza ɓoye mamakinka na ganina madaki, wannan da uban gayyar ka gani sai yaya kenan?". "Meya kawo ka wurina?" "Ahh ai ba abun faɗa bane ba, zuwa na yi na duba ya yanayin jikinka yake? Ni na hana mai zamani zuwa wurinka, da yazo nan da wani zancen ake yi ba wannan ba. Zuwa yanzu na san kana mamakin ina lakwari, kuma ya aka yi muka san in da kake? Lakwari dai Macijin nan mai ban tsoro viper, ya saya shi a cikin raminsa, sannan indabo yanzu ba ta taka yake yi ba, dan haka yanzu zaɓi ya rage gareka kafin mai zamani ya waiwayo gareka, ko dai ka fita ka nemi madafa, waɗanda ka zalunta su ƙarasa ka, ko kuma yunwa da wannan ruɓaɓiyar ƙafar taka su ƙarasaka a wurin nan. Ba zaka yi wa mai zamani wani amfani ba, saboda ya riga ya gama da kai, iya hakan nan da ya barka azaba ce mai zaman kanta, sannan ka sani, duk in da ka motsa ka tafi, yana sane da in da ka ke, ɗaukar fansa cikin ruwan sanyi" ya ƙarasa maganar yana ciro wata zabgegiyar wuƙa daga ƙugunsa. Madaki ya zaro ido ya ce "Kar ka matso in da nake, kar ka zo in da nake" yayi maganar yana dakatar da walid, dan idan yayi kyakykyawan yinƙuri, ji yake kamar naman cinyarsa zai zaftare ya faɗi. Babu tausayi, Walida ya kwarfe shi, ya danne shi a ƙasa, ya zana masa V a gadon bayansa da wuƙar hannunsa. Ya ce "Ka ce labarin Viper ba zai cika ba, sai an ambaceka, to kai kuma har ka ƙarƙare rayuwarka kana dakonsa da alhakinsa a kanka da gadon bayanka. Ka shirya a kowane lokaci zamu iya yi wa waɗanda ka zalunta cunenka. Kuma ina yi maka Albishir da hukuma ta kama tabar wiwinka da ƙwayoyi, baka ga tsuntsu ba ka ga tarko madaki" *** Nabila ce tsaye a falo, tana yi wa Nasir magiya. "Dan Allah Dsp ka bani wayoyina, ina buƙatar cigaba da amfani da su, ga ayyukana a ciki, amma ka riƙe mini waya da system ka hana ni" Ya kalle ta ya ce "Ba dai da wayoyin ki ke janyo wa kanki matsala ba, kin yi sallama da su, ba zaki sake riƙe waya a gidan nan ba, and beside gaba ɗaya ni ban yarda da ke ba, akwai abun da ki ke aikatawa wanda ki ke ɓoyewa". "Dan Allah ni ka bani wayoyina, ya za ayi ka karɓe mini kayan aikina, yaya wai meyasa ka ke yi mini haka ne?" "Ni ki ke ɗagawa murya haka?" "To ka bani mana" Abba ne ya shigo falo ya ce "Haba arfa, daga farfaɗowarki daga ciwon ki ke ta ɗaga murya har haka, sai numfashin ya sake samun matsala" "Abba kayan aikina ya ɗauke mini, ka ce ya bani wayata da system ɗina" Mama a ƙule ta ce "Dan ubanka ka bata kayanta, ƙannanka babu wanda ya isa yayi maka abun da take yi maka, da sun motsa sai hantara da zagi, amma kalli abun da take yi maka" Abba ya ce "Tsaya, Nasir meyasa zaka kaeɓe mata kaya ka hanata?" "Abba nayi seizing wayoyinta ne for a while, da su take amfani take janyo mana magana, haryanzu ba a tabattar da musababbin tashin wutar nan ba, amma zai iya yiwuwa saboda abubuwan da take yi ake neman sabauta rayuwarta". Abba ya ce "Haka ne, kana da gaskiya, amma ka yi haƙuri ka bata, ke kuma ki kiyaye da abubuwan da zaki din ga aikatawa da wayar nan, idan ba haka da kaina zan ƙwace su aikin ma ki daina yin sa. Bi shi ya baki kayanki" Nasir ya numfasa, yayi gaba ta bi bayansa, ya ɗaukko ya miƙa mata yana kallon idonta cike da tuhuma. "Wuƙa garin tone-tone take tono wuƙar yanka kanta, yaya, ina martabaka da martaba zumuncin da yake tsakanina da kai. Bana son harkar aiki ta zama tangarɗa ga wannan alaƙa da na lissafa maka, bayani ne nake yi maka da manyan baƙaƙe a kan farar takarda, sai dai ba zaka gane nufina a yanzu ba, ko dai ka bari a haka, ko kuma lokaci ya zo da fassarar da ba ita kake buƙata ba, ina fatan idan lokacin ya zo, zaka tuna wannan bayanin nawa, kuma ba zaka ga abun a bazata ba". Ayshercool 08081012143 65 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin rashin fahimta, yake bin ta da ido, sai dai tamkar soko, har tayi maganar ta gama, bai iya tofa mata uffan ba, har tayi ta gama ta karɓi wayoyinta da system tayi tafiyarta ɗaki. Ɗakin ta rufe, ta shiga duba call logs ɗin ta, amma kaf ba ta ga kiran Viper ba, wani irin takaci ne ya turnuƙe ta, wato duk siraɗin nan da ta tsallake da kyar, bai kirata ba, balle ya ji a wane hali take ciki. 'To idan kuma bai san abun da ya faru ba fa?' ta tambayi kanta. Ta basar ta ce bari ta jira zuwa gobe, taga ko zai kira wayar. Ƙasan zuciyarta kuma ta din ga hamdala da Allah ya sa bai kira ɗin ba, dan da ya kira Nasir zai ɗaga ne, kuma ba abun da yayi masa zafi, zai iya gaya masa waye, idan ya tambayi waye. *** "Naja wai ko ke ki ka saka aka yi wa yarinyar nan wani abu ne?" "Wace yarinyar?" "Barrister nan? Karofi ya kira ni yana yi mini kashedi, ina tsoron Allah ina tsoron shu'umancin mutumin nan" Naja ta ce "Eh, ni na saka aka yi mata haka, dan so nayi ma ta mutu, na ga kai ka ƙi mayar da hankali ka yi abun da yakamata, ba zai yiwu ta tona mini asiri a banza ba, mutuncina ya zube a idon duniya ba. Ba a taɓa samun wanda ya yi yinƙurin kawo mini tangarɗa ba, ka ƙyale shi ka ke jan ƙafa a kansa ba, sai a kan wannan yarinyar" A fusace Indabo ya ce "wai meyasa ki ke haka ne Naja? Duk iya ƙoƙarin da nake yi a kan lamarin nan? Na gaya miki zata iya zama tarkon da zan kama Viper, kuma ina amfani da ita wurin yi wa yayanta barazana yake yi wa umarnina biyyaya, lokaci ɗaya karofi ya bijiro, yake yi mini gargaɗi a kanta, wai sonta yake yi, wataƙila ma yi yake yi dan kawai ya muzanta ni. Amma gaba gaɗi babu shawara, kin je kin aikata abu, kin saka yana ta kiran wayata yana nema ya tozarta ni" "Nifa ban yi danasanin abun da nayi ba, kuma zan cigaba da bibiyarta sai na ga bayanta, ban damu da abun da zai biyo baya ba muddin zan tsira, kar ka manta kai ka koyar da ni hakan" ta kaste wayar tana jan guntun tsaki. *** A gurguje Abdul ya yi breakfast a wurin ramma, yayi mata sallama ya fice. Bayan fitarsa ta daɗe tana kuka, kamar zuciyarta ta fashe haka take ji, saboda damuwa da tashin hankali, tun tana lissafin adadin kwanakinta a wurin Abdul, har ta karaya lissafi ya ƙwace mata, tana matuƙar son sanin halin da mahafiyarta ke ciki. Ta sha attempting ta saka wuƙa ta kashe Abdul, amma sai ta kasa, ita kanta ta sha yinƙurin kashe kanta, amma tuna makomarta sai ya sanya ta fasa. Gashi yanzu sam ba ta iya bujirewa buƙatar sa, rayuwa suke yi tamkar ma'aurata, ta yi kuka tayi istigfari amma da ya zo ya kalallameta da zance, sai ta bayar da kai bori ya hau, wasu lokutan idan ta kalli hidimar da take yi masa, ta gyaran gida, kula da abincin sa, yin wani abu da zai saka shi farinciki sai ta yi sai ta ji haushin kanta ya isheta. Abdul kuwa Asibitin su doctor AK ya wuce, ofishin sa ya je suka gaisa ya ce "Kai ne zaka yi morning kenan?" Ak ya ce "Eh ni ne your excellency kai fa zuwa yanzu ya ci ace ka ajiye Lab coat, tun da ana ta ƙishin-ƙishin kai ne zaka zama lamba biyun garin nan, zaka koma field ɗin dadynka" Abdul ya ce  "Nifa Ak ko lamba ɗayan ƙasar nan na zama, ba zan iya daina aikin likita ba, ina gudanar da office ina consultation" suka tafa tare da kwashewa da dariya tare. Ak ya ce "Sannu doctor excellency, ina ƙanwar ka da kuka zo tare kuwa? Baka wani tsaya mun gaisa da ita ba, ko dan kar na ƙyasa ka bani ita, ai ban taɓa sanin kana da ƙanwa ba, na zata kai ne ƙarami" Abdul ya tsuke fuska ya ce "A wane room patient ɗin take ne?" "Ai ta uzzura sai da aka sallameta, amma Alhamdilillah jikinta yayi kyau sosai, sai dai ka yi mana ward round idan da abun da za a taimaka mana ayi mana" ya jinjina kai ya juya ya fice daga office ɗin. *** Tun bayan da ɗan mama ya tabattarwa Viper an sallami Nabila daga asibiti, yake kallon wayarsa yake jiran kiran wayarta, amma shiru ba ta kira shi ba, har ya fara tunanin ko ƙarya ɗan maman ya yi masa da ya ce ta warke an sallame ta. Shigowar Walid ce ta dawo da shi hayyacinsa, ya ɗaga kai ya kalle shi, Walid ya ciro wuƙarsa ya zareta daga cikin gidanta, ya kalli Viper ya ce "Lakwari da gaske yake, na iske madaki, ƙafarsa ba ta takuwa, raunin da ka yi masa ya zama gyambo a ƙafarsa, ga shaida harafin sunanka na zana masa a gadon bayansa, yadda shi ma ba za a kammala na sa labarin ba, dole sai an ambaceka" Viper yayi kamar zai yi murmushi ya ce "Mai laya" Walid ya ce "Na kiyayi mai zamani, Allah ya kiyaye mini kai ɗan amanata" Viper ya ce "Ina kewar wancan kwanakin, kwanakin da aka yi rashin ji da gaske, yanzu girma ya fara zuwa duk an daina wasu abubuwan" Walid ya yi murmushi ya ce "Rashin jin ai duk ba na daɗi bane ɗan uwa, duk da kai ƴar madara ta fara saita mana kai, Allah ya karɓi kayarsa, amma duk da haka ba zan gushe ba ina jinjinawa Nabila, dan ita tayi abun da muka kasa, albarkacinta mun sake ganin walwala a tare da kai, duk da ba ta kai ta wancan lokacin ba" "That angry bird, masifaffiya" ya furta yana kallon liti ya ji me zai ce. Aikuwa kamar mai jiran ƙiris hya e "Ba wata tsiya da ta tsinana masa, sai shegen naci da taurin kan tsiya, mara kunya da ita sai kayan ƙaton kai kamar injin markaɗe da ƙwala-ƙwalan idanuwa kamar an soya aya, ai wallahi 'yar madara duniya ce, ga kunya da girmama mutane, wannan tsagerar kuwa, tana zazzarewa mutane ido, ni har mamakin mai zamani nake yi wallahi". Walid ya ce "Ai ita ce daidai da ku, daga kai har mai zamanin, mu da muka kasa iya masa, ita ai gata nan yana saurarenta" "Ba wani nan, ni haryanzu ba gama yarda nayi da ita ba, yar leƙen asiri ce" Walid ya ce "To tayi leƙen asirin, ai ba asirinka ta leƙa ba ko?" "Ware, ban da naga kuna ta tata, da sai na saka tsumagiya na jiƙa mata jikinta, sai na yi mata mazinacin dukan da ba zata iya tashi ba, na rama muguntar da yayanta yayi mini a station" Viper yana gefe yana jin su, wasu lokutan faɗan Walid da liti nishaɗi yake saka shi, kamar sako da sako. Nabila wuni tayi da waya a hannu, amma shiru babu kiran Viper, shi ma haka ne, wuni yayi yana kallon wayar ta sa yana sauraren kiran wayarta, amma ba ta kira ba. *** Nasir ne zaune a ɗakinsa, yayi zurfi sosai a cikin tunani, yana ta tuna wasu abubuwan da suka faru a 'yan kwanakin nan sosai yake jin yana zargin Arfa tana aikata wani rashin gaskiya, da take ɓoyewa, mussman da ya ji ta ambaci viper lokacin da ta farfaɗo, ba zai yiwu a ce magagi ne kawai ba, kuma a yan kwanakin nan tayi watsi da lamarin cewa zata taimaka masa a kan nemansa balle ya ce tsananin saka abun a ranta ne ya sanya ta farko da sunansa, amma haryanzu yana son sanin dalilin da ya sanya Indabo ya ce zai yi tarko da Nabila ya kama Viper, menene haɗinta da shi?. Nabila tana zaune a kan gado, tana waya da Alhaji Wada, sai kashe murya take yi, wai ita haryanzu ba ta warke ba, ya biye mata sai sangarta take yi, kamar ba babban mutum ba yana lallaɓata, tun da ya ce zai kuma zuwa gida dubiya ta ce masa ai ta warke ba sai ya zo ba. Sallamar baba magajiya ce ta sanya tayi masa sallama, ta ɗago ta kalleta da murmushi. "Yauwwa yar gari, ai dama zuwa nayi na tashe ki, ki samu ki karya ki sanya wani abun a cikinki, ashe ma kin tashi " "Eh hajjaju, ina kwana" "Lafiya lau, ya ƙarfin jiki kuma?" Nabila ta ce "Alhamdilillah da sauƙi" "To Allah ya ƙara kiyayewa, ki cigaba da addu'a Allah ya ƙara tsarewa, dama mu ma addu'a cikin yin ta muke babu dare babu rana, Hasbunallahu wa ni'imal wakil, ki yawata faɗarta babu adadi, da yardar Allah ba dai mutum ba sai dai Allah" Nabila ta yi murmushi ta ce "Kin faɗa kin nanata mini, na daɗe da haddacewa ai" "Kya ci ƙaniyarki da kin daɗe da haddacewa, zamanin nan na yanzu waya ce miki ana zama haka? Kana da ido ba na ganin gari ba, Addu'a kake tuƙuru iya yinka, baka san waye maƙiyin fili da na ɓoye ba" Sosai Nabila take dariya ta ce "Aikuwa maƙiyina yana ruwa, dan ni kaina ba wani cikakken saiti ne da ni ba in ji Abba" "Ke ki yi addu'a kawai yar nan, tashi ki je ki samu abun da zaki ci" ta saukko daga kan gadon, ta fice falo tana miƙa, wayarta take kallo lokaci lokaci, duk kiran Viper take jira, amma shiru. Sauda ta kalleta ta ce "'yar asara an fito" Nabila ta ce "Wallahi kuwa, Allah ya nufa barka da safiya, bazawara uwar son banza ga gadonki ga na asara" "Arfa, me ki ka ce?" "Sauda kin sani sarai bana shiru idan aka gaya mini babu daɗi, ni yanzu a kan tsini nake, magana ɗaya mara daɗi ki ka yaɓa mini, sai na yi miki goma mai zafi, ba girmata ba Allah ya sa haifata ki ka yi" Sauda za ta yi magana, ta jiyo takun Abba yana saukkowa daga kan bene, dan haka ta haɗiye maganar ta, tana kallon Nabila. *** Abbu ne zaune a gefen gadonsa, fuskarsa sanye da farin glashi, ya zubawa hoton hannunsa ido. Shi da Zahra'u ne, da sadik, shi kuma hannunsa riƙe da Al'amin, bai fi shekaru biyu ba a lokacin, sai dai fuskar nan ta sa tamau, babu alamar fara'a. Murmushi Abbu yayi, tun Al'amin yana yaro baya son wargi, ba shi da faa'a, ya tuna yanzu a jikin hoton ba kowa sai Al'amin, shi ma ga yadda ya zama, rabon da ya saka shi a idonsa, tun fitowarsa daga prsion da ya zo masa nan, kusan shekara guda kenan. "Wai meyafaru ne kamar kuka fa kake yi?" Ya ɗaga kai ya kalli rahila ya ce "Kuka kuma?" Ta leƙa ta kalli hannunsa, ta kwaɓe baki ta ce "Kai ta wani abu kamar ƙaramin yaro, ka ɗauki hoto ka saka a gaba kana kuka, haba kai kuwa?" Yayi mata shiru bai ce komai ba. "Abbu, dan Allah magana nake so mu yi da kai" "Ina jinki" "Dan Allah ka yi haƙuri ka yafewa Abba, ya koma kasuwa, sai raragefe yake yi a gari da shi da Nazifi, ina tsoron kar su faɗa wani mummunan halin, rashin sana'a ga matashi babbar matsala ce". Ya ƙare mata kallo ya ce "Rahila, nawa ɗan ma da ya kangare, sallama shi nayi, ba zai yiwu in cigaba da jan ɓarayi a jikina suna zalunta ta ba, su yi ta yawo babu sana'ar, ai uban su yana raye, ya nemi abun yi ya ba su" "Ni kake kallon idona ka ke cewa yarana ɓarayi?" "Na faɗa rahila, ba ɓarayin bane ba? Wane irin gata ne ban yi musu ba, ƙarshe rashin lafiya na kwanta aka rasa wanda zai zauna da ni a cikin su a asibiti, ƙarshe cewa ki ka yi kar na ga laifin su, ba hakkinsu bane ba, amma ni na riƙe su na ciyar da su, na kula da su, ni nawa hakkin ne? Yanzu nake ƙara danasanin biye miki, na wofantar da nawa ɗan, kuma ki tattatara su gaba ɗaya su bar mini gida, dan ba hakkina bane ba riƙon su" Cikin takaici ta ce "Wallahi ba zan rabu da 'ya'yana ba, sai dai na tattara da ni da su mu bar maka gidan" "Allah ya raka taki gona, ya tsare hanya" Cikin fargaba ta kalleshi ta ce "Au babu ruwanka kenan in tafi baka damu ba?" Tashi yayi, ya ja tsaki ya mayar da takardun gabansa ya bar ɗakin. *** Nabila ta kasa jurewa, hankalinta ya fara tashi, ko wani abun ne ya samu Viper, duk da bai fiye kiranta ba, sai da ƙwaƙwƙwaran dalili, amma shirun yayi yawa. Yau take shirye-shiryen komawa wurin aiki, Barrister Habib ya tabattar mata da an gyara office ɗin ta, an canza mata wani. Har ta shirya ta tsaya, ta kira lambar Viper. Yana kwance idanunsa a lumshe, yana ɗan kaɗa ƙafa, ya ji ringing ɗin wayarsa. Ganin lambarta sai da ya yi ajiyar zuciya, amma ya zubawa wayar ido, sai da ta kusa katsewa, sannan ya ɗaga kuma yayi shiru. "Hello Viper" "Salamu alaikum" ya faɗa a nutse. "Wa'alaikum Salam, kana lafiya?" "Ƙalau" Cikin marairaicewa ta ce "Wai baka san abun ya same ni bane ba? Kwana nawa baka ga kiran wayata ba baka neme ni ba, wrong connection na wearing aka yi a office ɗina, wuta ta shi, aka rufe ni ta waje fa" "Na sani" "Ka sani?" Ya ce "Eh" Cike da takaici ta ce "Kuma ka kasa nemana a waya, da mutuwa na yi fa" "Allah ya jiƙanki, zahra ma da mutu haƙuri nayi, balle ke. Sai ki ƙara taka tsantsan da abubuwan da ki ke yi" Wani ƙululun takaici, ya tokare mata wuya, sosai ta ji zafin abun da ya ce mata, kawai ta katse wayar. Walid ya ce "Viper, kamar baka kyauta ba fa" yayi masa shiru, hakan ya sa shi ma yayi shirun bai kuma cewa komai ba. Baƙin ciki da ɓacin rai ya sanya, babu wanda ta yi wa sallama a gidan ma, tayi tafiyarta. Tana tafe a hanya ta din ga jin wani abu mai kama da kishi, da ɓacin rai yana taso mata, har ga Allah ba ta san jauhar ba, amma tana son ta saboda Allah, amma abun da yayi mata yau, ya sanya ta ji ranta ya sosu. "Meyake damuna ne? Wai son bawan Allah nan nake yi? Na shiga uku me yake shirin faruwa da ni ne? Idan ta tabatta son shi nake yi, na yi wauta, to yaya ma za ayi hakan ya yiwu abu daga wasa?" Har ta ƙarasa wurin aiki, tunani take a zuciyarta. Tayi shiru tana sauraren zuciyarta dan ta tabattar da abun da take tunani gaskiya ne ko akasin haka, amma bata kai ga hakan ba, aka ƙwanƙwasa glashin motarta, masu gadi ne suke yi mata barka da dawowa, tare da yi mata sannu da jiki". Ta saukko daga motar, suka gaggaisa, sannan ta shiga ciki, a cikin ma murnar ganinta suka din ga yi suna yi mata sannu. Ko mintuna talatin ba ta yi a sabon office ɗin ba, barrister Habib ya ƙaraso. "Autar lauyoyi, ƙaramar su babbar su, aminiyar sumy, ƙaramar sauro ka da ƙatuwar giwa, ba giwar ba hatta toron ma kayarwa ki ke yi" Nabila ta yi murmushin yaƙe ta ce "Ni har ka bani kunya ma" "To yaya jikin naki?" "Alhamdilillah yayi sauƙi sosai" Ya ce "Masha Allah, yanzu ya ake ciki da batun shari'ar nan? Zamu je prison ɗin ne wurin mutumin?" "Za a bari mu ganshi kuwa?" Habib ya ce "Za'a bari mana ba dole ba, ai na je lokacin kina gadon asibiti, ba na son abun da zai kawo tsaiko a harkar shari'ar gaba ɗaya"  "Kai amma na gode sosai yaya habib " "Kar ki damu Nabila, ba ke ba, hatta ni na ji haushin yadda shari'ar nan ta gudana, kuma cin mutuncin harkar shari'a ne, a wannan karon zamu yi nasara in sha Allah " "Allah ya sa yaya Habib" suka fito suka hau motar barrister Habib suka fita. Nasir da yake bin Nabila a wata motar, ya ga fitar Barrister Habib da Nabila, ya sake rufa musu baya, sannu a hankali ba tare da sun san yana bin su ba, sai dai azabar kishi ya sanya ya ji har wani dishi-dishi yake gani. A wannan karon Nabila tayi mamakin yadda aka basu damar ganin baba maigadi, ba tare da an raina mata hankali kamar yadda aka saba ba. Suka gaisa cikin mutuntawa, duk ya rame yayi wani iri. "Baba, ina mai sake baka haƙuri, amma ban karaya ba, in sha Allah zamu ɗaukaka ƙara ne" Jiki a sanyaye Baban ya ce "Kina ta ɗawainiya, ni idan babu hali, kawai a bar maganar nan, na bar wa Allah" Barrister Habib ya ce "No ba zai yiwu ba, ka manta yadda muka yi da kai wancan zuwan da nayi muka haɗu?" Yayi shiru ya sunkuyar da kai. "Ka yi magana mana, mun yi magana da kai fa sosai baba, ka bata haɗin kai dan Allah, a wannan karon muna fatan ayi nasara, ka yi mata bayani, saboda ƙoƙarin kamanta gaskiya har nema aka yi a sabauta rayuwarta, ka yi magana baba, ka yi mata bayanin komai. Nabila let's record it Incase" Ta jinjina kai ta ɗaukko wayarta, ta danna recording ta ajiye. Cikin tsoro ya ce "Dan Allah to kar ku gaya wa kowa, kun ga yarana duka mata ne, na aurar da wasu, ina da biyu ƴan mata, an ce muddin na yi magana abun da ya samu ramma zai same su, koma su rasa rayukansu gaba ɗaya tsoro nake ji" mamaki ya cika Nabila, dan ita duk bai yi mata wannan maganar ba. "Baba, ni na baka tabbacin nan, babu abun da zai samu iyalanka, ka ba ta cikakken haɗin kai, idan ka bari ta sake faɗuwa a shari'ar nan, kaga magauta sun yi galaba a kanta, kuma yayan da ka ke yi wa, ka ɓata musu suna" Ya jinjina kai ya ce "Ana saura kwana biyu uwar ɗakin hajiya jidda, tayi waya ta ce aje garin su ramma, ta dawo su haɗu da ɗaya mai aikin, ayi mata gyaran gida, saboda tana ji da Ramma sosai, tana da biyayya, kuma bata yi mata sata. Ranar an ɗaukko ramma, suna ta aiki, zulai ta tafi kasuwa, ɗan yayar matar gidan ya zo, sunansa Abdul, ban daɗe da fara aiki a gidan ba, dan babban mutum ne sosai mutumin, in da suka baro, jami'an tsaro ne suke yi masa gadi. Unguwar nan da suke ne, jami'an tsaro layuka suke gadi, ni kuma aka samo mini buɗe ƙofa da rufewa a gidan. Bayan yayi mata, ya tafi zulai ta fito tana kururuwa, bayan ta dawo daga wurin sayen kayan miya. Bayan mun kai ta Asibiti, magana ta bazu, aka ce an sallame ni daga aiki, amma za a neme ni, daga baya yan sanda suka je gidana suka tafi da ni, wai zan ba da bayanin abun da na sani, muna zuwa aka rufe ni aka ce ni ake zargi, kuma aka yi mini barazana da muddin na ce bani bane ba yarana na cikin haɗari" Nabila ta ƙulu ta ce "Amma meyasa baka yi mini wannan bayanin ba ni, na san ta ina zamu ɓullowa lamarin? Nayi ta wahalar neman shaida ka kuma ƙi bayani a kotu" Barrister Habib ya ce "Kwantar da hankalinki, ki yi haƙuri kin san uba da 'ya'ya" "Ki yi haƙuri na san nayi kuskure amma a tsorace nake ne nima" Ta kalleshi ta ce "Ya sunan mai gidan?" Ya girgiza kai ya ce "Ban sani ba" "Ya za ayi ka yi aiki a gidan wanda ba ka san sunansa ba?" Yayi shiru ya sunkuyar da kai. Barrister Habib ya ce "Tashi muje, ma ƙarasa sauran aikin" haka suka fito Nabila tana mita, barrister Habib yana bata haƙuri. Law firm ɗin suka koma, suka fara arranging ɗin yadda zasu yi appeal, sun gama ta fito suka haɗu da barrister Kabir, yayi mata sannu, tare da yi mata kashedi, a kan ta raba kanta da aikata duk wani abu da zai sanya ta shiga matsala, ta bishi da to, ta fita ta shiga motarta ta nufi gida. Nasir bai ga wani abu ba a bibiyar Nabila da ya yi yau ba, amma bai ji zuciyarsa ta gamsu ba, ya sakawa ransa zai yi assigning wani wanda zai din ga bibiyar masa ita lokaci zuwa lokaci. *** Su liti suna karyawa, Viper kuwa yana zaune yana yanke farcensa da nail cutter. Wayar liti aka kira, ya karɓa ya ɗaga ya ce "Ya ne?" "Normal, kwana biyu ba ku shigo gada ba fa" "Eh ka san yanayin ne, sai muna bayyana muna ɓacewa, meye labari?" "Baban Viper ne ya zo rumfa, ya na neman ka, ko kai ko walid" liti ya kalli walid ya kalli Viper. "Meyafaru yake nemanmu?" Ya ce "Ban sani ba, ya dai tambaye mu, ko Viper yana zuwa wurin, muka sanar masa rabonmu da shi, tun kafin a kama shi, shekara shida kenan" Liti ya ce "Normal ne, zan faso fatan rumfa komai lafiya?" "Lafiya ƙalau tana ta garawa" Ya jinjina kai ya ajjye wayar. Liti ya cigaba da kallon Viper, Viper bai kalle shi ba ya ce "Ko dai ka yi magana, ko kuma ka daina kallona" "Allah ya baka haƙuri, na daina kallonka" kamar ya gaya wa Viper, zuwan mahaifinsa rumfar shayinsu, sai kuma ya fasa ya haɗiye maganar. *** Abdul ne yayi sallama a falon, ya shigo a gajiye, ta amsa sallamar tana tashi zaune daga kwancen da take. Ya ajiye jakarsa, ya kwanta a jikinta ya ce "Wash" Ta ce "Sannu" "Yauwwa sweetheart" ta kama hannunsa, ta cire masa agogon hannunsa. "Tashi a cire safar" "Ki bari na huta na gaji" Ramma ta ce "Ƙato da kai kana shagwaɓa, wataƙila ma ba wani aiki ka yi ba kake wani wash" Ya ce "Kaii, baby kin san mutum nawa na yi wa tiyata kuwa? Ga kusan asibiti uku naje na ga marasa lafiya" "To tashi ka yi wanka, ka ci abinci" ya kalleta ya yi murmushi ya tashi zaune, ya shafa kanta ya ce "Allah ya yi miki albarka babyna, i so much love you" yayi maganar yana sumbatar goshinta. Kallonsa take yi, tana son jin matsananciyar tsanarsa a zuciyarta, amma abu ya gagara, sai wani ma kyau da ta ga yayi mata. Ya tashi ya tafi bedroom, yayi wanka, Ramma ta goge hawayenta tana fatan Allah kar ya jarrabeta da son Abdul. Yayi salla ya fito, ta bashi abinci. "Beb, in sha Allah komai ya kusa zuwa ƙarshe, zan bayyanawa duniya ke, ina daf da gayawa babana maganarki, a san yadda za a gyara lamarin mu cigaba da rayuwarmu, am ready na ɗauki kowane risk mu zauna tare in sha Allah my rahama" Tayi ajiyar zuciya tare da murmushi. "Dan Allah ko sau ɗaya ki ce kina so na mana" "A'a ni ban iya ƙarya ba" Ya ce "Zaki yi bayani ne" *** "Hello masoyiyyata" Nabila ta ce "Na'am sumy kalar kyau" "Albishirinki?" "Kuɗi dubu goma" Sumayya ta ce "Mayyar kuɗi, ba za a bayar ba" Tayi dariya ta ce "Fesa mini" "Arfa ranar monday in Allah ya kaimu, zan fara aiki, ni da yaya murtala zamu buɗe gidan radion" Nabila ta miƙe ta ce "Dan Allah masoyiyya" "Wallahi da gaske, ke Allah ne ya kawo mana mafita, an bani damar ƙirƙirar programs, har na sami program ɗin da zamu din ga yi tare, mu ci karenmu babu babbaka, babu mai yi mana barazana da daka tsawa". "Ke gani nan zuwa gidan naku ma, tare da ni za a buɗe gidan rediyon nan in sha Allah" Duk wannan abubuwan da Nabila take yi, ƙarfin hali ne kawai, zuciyarta na tare da Viper, tunaninsa kawai take yi, tama rasa wane irin tunani take yi a kansa, ga zuciyarta da take ta azalzalarta da son ganinsa. Tare da Nabila aka yi bikin buɗe sabon gidan radio, mutane suka din ga kiran wayar suna yi wa Sumayya fatan alkhairi, tare da tabattar mata da duk in da ta tafi suna tare da ita. A program ɗin farko da suka fara yi da sumayya, suka sanya masa suna ƙeƙe da ƙeƙe. Tun da sumayya ta gabatar da Nabila, kasancewar masu saurare sun santa a bakin sumayya, suke ta tura saƙonnin gaisuwa, wasu kuma suna tambayarta dalilinta na ƙalubalantar bunkure foundation, duk da irin gudunmawar da take bawa al'umma. Sumayya ta ce "Masoyiyya, kin ji tambayoyin masu sauraro mai zaki ce?" Nabila ta yi murmushi ta ce "Babu abun da zan ce, sai su kasance da mu a sabon shirinmu, na ƙeƙe da ƙeƙe. Ba wai bunkure foundation ba, duk wani abu da ake kitimurmura a cikin sa, ko rashin adalci zamu yi bajekolinsa a wannan shiri, kuma program zai iya bi ta kan kowa, duk wanda ya ga kuma an yi masa ba dai-dai ba ya ƙalubalance ni a gaban shari'a. Manyan shari'oi da aka yi bita da ƙulli a ciki, yadda ake danne hakkin mara galihu ake tsayawa yaran masu kuɗi, yadda ake wasa da hankalin talaka, da tauye masa hakki, shi fa wannan program ɗin, kai har da shari'ar wani gawurtaccen matashi da ya shahara, jami'an tsaro suna nemansa, sai dai abun mamaki shi ne sai da ya shafe shekaru biyar ba ayi masa shari'a, a shekara ta shida aka sake shi, kuma yanzu an ce ba bisa ƙa'ida aka sake shi ba wai nemansa ake yi. Akwai tarin kwamacla a harkar shari'a a ƙasar nan, a shirin ƙeƙe da ƙeƙe zamu fayyace abubuwa da dama, na ban mamamki" suka ƙarƙare program ɗin cikin wasa da barkwanci. *** Alhaji wada hankali kwance yake zaune yana shan lemo a kofi, yana kallon indabo da yake ta haƙilo yana magana. "Karofi, ka shiga gonata da yawa, ka kiyayeni, muddin kana son yarinyar nan ta rayu, ya zama dole ka takawa shirin nan da zasu fara gabatarwa burki" Karofi ya ce "Sabod me? Kai da kake ɗaukar nauyin gidan radion ka ake abun da ka ke so waye ya hana ka? Ni na ɗauki nauyin program ɗin dan haka babu ruwanka da abun da ake yi" "Karofi, ka san na fi ƙarfin kafi ga bayana ko?" "Ai ka san shi ƙarfen cikin wuta sai da ɗan uwansa ƙarfe, babban mutum mai kima a ƙasar nan, bai kyautu ace ka na ɓata lokacinka a kan wata ƙaramar alhaki kamar wannan yarinyar ba. Auuu ashe fa ta sako wani zance a maganarta, mai kama da maganar Al'amin Viper, wato mai zamani. Kana tsoron ta tona maka asiri cewa kai ne ka saka aka kashe matar Viper ko? Ka kwantar da hankalinka ba ta san wannan labarin ba, idan har ba tana haɗuwa da Viper ba ya gaya mata da kansa" Wani irin shock indabo yayi, ya sandare a tsaye, jin yadda Alhaji mu'azzam wada kankarofi yake farke sirrin da bai taɓa tunanin wani mahaluki ya sani ba. Ayshercool 08081012143 66 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Indabo da ƙyar ya iya buɗe bakinsa ya ce "Kankarofi" "Indabo" "Wace irin magana kake faɗa ne?" "Irin wadda ka ji da kunnenka, ka zata daga kai sai waɗanda kuka aikata laifin ne ku ka sani? Kamar na so na fika iya playing cards ɗina ko?" Indabo zai yi magana, Jidda ta shigo wadda ita ce matar kankarofi, kuma ƙanwar indabo. "Yaya yana ganka a tsaye ne? Ba dai har tafiya zaka yi ba?" Kankarofi ya ce "Eh, ya ce tafiya zai yi, dama ziyarar ta bazata ce, mu je na taka maka" kamar wawa haka indabo ya bi kankarofi suka fito. Ya sake kallon indabo da yake ta rarraba ido, kamar shege a rabon gado ya ce "Ka fa kwantar da hankalinka, kar ka yi zaton zan gaya wa wani wannan sirrin tsawon shekaru  kenan, ina dakonsa ba wanda ya sani, ko ma na faɗa bani da wata ƙwaƙƙwarar hujja a kai, ina gargadinka ne kawai ka kiyayi yarinyar nan". "Kankarofi" "Indabo" "Hawainiyarka ta kiyayi ramata, sanin wannan sirrin ba shi yake nufin kana da lago na ba" Kankarofi ya ce "Na sani, na ankarar da kai ne kawai, na san abun da kake yi, dan haka kar ka tsallake gona da iri". Indabo kawai ya jinjina kai zai juya ya tafi, Kankarofi ya ce "Na san zaka yi mamakin yadda aka yi na sani ko? Ba abun mamaki bane ba, kar ka je ka sakawa kanka damuwa da dogon tunani" bai ce masa komai ba, ya yi gaba. *** Abdul yana kwance yana bacci, saboda daren jiya bai yi bacci ba, ramma tayi bacci, aka kira shi asibiti, sai bayan sallar asuba ya dawo. Ramma ce ta shiga ɗakin a gigice, tana dukansa a kafaɗarsa. Ya buɗe idonsa ya ce "Meye haka kuma?" "Ka tashi" "In tashi in yi miki me? Rahama ban yi bacci ba fa jiya, ina asibiti". A gigice ta ce "Ina ruwana? Abdul ban ga al'ada wancan watan ba, wannan ma lokaci ya wuce" "Kuma shi ne zaki tashe ni ina bacci?" "Dole na tashe ka, me hakan yake nufi ka tashi ka duba ni, ba zan sake ɗaukar ciki ba, ni ka tashi ka duba ni" Tashi yayi daga kan gadon, bai ce mata komai ba, ta bi bayansa tana kiran sunansa, amma ya rigata fita ya kulleta a ɗakin, ya tafi wani ɗakin ya yi kwanciyarsa. *** Sosai sumayya take jan jama'a a sabon gidan radion da kama aiki, da ita da murtala. Saboda bayan kasancewar ta sananniya, tayi ƙoƙari wurin samar da sabbin shirye shirye masu ƙayatarwa, wanda za su tafi dai-dai da matasa da ma dattijai baki ɗaya. Wasu daga cikin abokan aikinta da ta baro a can, suka din ga yi mata magiyar suma ta samar musu gurbi a in da ta koma, suma su koma. Yanzu sumayya ba ta da fargabar ta samo rahoto, a kushe ace mata ba irinsa ake buƙata ba, saboda kawai bai yi dai-dai da abun da wasu suke son ji ba. Ranar farko da suka gabatar da program ɗin ƙeƙe da ƙeƙe ita da Nabila, program ɗin ya yamutsa hazo,  dan tayi sukuwa tayi zamiya, ta ƙarewa bunkure foundation ta tas da hukumar shari'a, tayi bayanin yadda shari'ar baba mai gadi ta kasance a kotu, tare da jaddada idan har da gaske dan al'umma suke ayyukansu, ya zama dole a bayyana ina ramma take, idan kuma da gaske tana asibiti, a bawa lauyoyi da ƴan jarida damar zuwa su ganota, kuma a kawo bayanin likita a kan abun da yake damunta zuwa lokacin da aka gaza ganinta a gaban kotu. Hatta lauyan gwamanti ta din ga challenging ɗin sa, a yadda suka din ga taka doka yadda suke so. Nan fa mutane suka din ga tururuwar kiran waya, wasu suna sharhi, ciki har da wani lauya mai zaman kansa, da ya kira waya, ya tofa albarkacin bakinsa tare da tabattar da akwai jabun lauyoyi da suke yi wa doka hawan ƙawara, a yi cuwa-cuwa a danne hakkin mai ƙaramin ƙarfi, a wanke yaran masu ido da kwalli, ire-iren foundations ɗin bunkure suna da yawa. Ya ƙara faɗaɗa bayanan da Nabila tayi, tare da fito da wasu abubuwa ma da ita hankalinta be kai, kai ba. Nabila ta ji daɗin program ɗin sosai da sosai, dan kuwa ji tayi, zuciyarta ta rage raɗaɗi da baƙin cikin abun da aka yi musu a kotu. Bayan kammala program ɗin, still cigaba da kiran wayar a aka yi, ƙarshe sai kashewa suka yi. Sumayya ta ce "Mutuniyata kin yi bala'i fa" Nabila ta ce "Ke ni ɗin ta wasa ce? Ai sai Najar bunkure ta zubar da hawaye, yanzu ta ƙarƙashin ƙasa zan yi analysis nawa ƙungiyar take samu na tallafi a wata, da kuma abun da ake spending wurin tallafwa mutanen da ake iƙirari. Ni ɗin fa ba ta wasa ce ba" Sumayya ta ce "Ba wani ta wasa ko ba ta wasa ba, dole mu daga da Addu'a fa, Allah ya tsaremu Masoyiyya" "Amin dai, amma yanzu meye abun yi?" Sumayya ta ce "Eh to, kamar yadda ki ke tunanin kawo ƙarshen bunkure, ni kuma sonake na ci uban indabo, duk da ya fi ƙarfina, amma zai ga abun da 'yar matsiyata zata iya yi, dan wallahi sai na kusa girgizo shi daga kan kujerar nan" Nabila ta kwashe da dariya ta ce "Me yayi miki ne, ki ke wannan alwashin?" "Zagin cin zarafi yayi mini, lokacin da ya ce na din ga bibiyar masa ke, kin san na taɓa zuwa na bayar da wani rahoto, a kan cewa an ce an yi wani aiki a yankinsa, kuma da na je ban tarar an yi ba, kin ga abubuwan da aka yi mini a kan hakan? Program ɗin da zamu din ga yi da yaya murtala, irin su Indabo zamu din ga bankaɗawa asiri. Zamu faɗi abun da suke karɓa na consituency project duk wata, da kuma ayyukan da suka gabatar a watan, daga nan ya ragewa al'ummar yankin da ake wakilta, su yanke hukuncin da ya dace" "Allah ya ƙara lafiya, ƴar gwagwarmaya amma shirin ya ƙayar da ni, Allah ya taimakemu ya ƙarfafi gwiwarmu masoyiyya. Abun mamaki shekarun baya bamu taɓa tunanin samun wannan damarmakin ba, sai dai mu yi ta dama dama" "Haka lamarin Allah yake, yanzu ya ara mana damar da muka roƙa, ya rage namu mu yi abun da ya dace da ita" "Haka ne, Allah ya taimake mu ya bamu sa'a" suka ce Amin. Ko da ta koma gida, Walida ce ta fara tararta ta ce "Arfa, yanzu muka gama jin program ɗin ku, live ku ka yi shi, kina ta ɓarin maganganu ko tsoro ba kya ji" Nabila ta ce "Walida, wanda bashi da gaskiya ai shi ne yake tsoron a faɗeta, bamu fara dan mu daina ba" "Zaki ga baki fara dan ki daina ba, yaya ya shigo a ƙalla sau uku yana nemanki, ya kira wayarki ma, kin ƙi ki ɗaga" "Duk a kan program ɗin da na yi" Walida zata bata amsa ya shigo, fuskarsa babu annur ko kaɗan. Ta tsaya tana kallonsa, ya ƙaraso gabanta ya kalleta ya ce "Arfa ba zaki taɓa yin hankali ba ko? Meyasa ki ke son yin wasa da rayuwar ki ne?" "Dsp, rayuwa ta ka ce ai, nikaɗai nake abuna ai, shiyasa nake takatsantsan kar baya tawa rayuwar, na saka ta wani a hatsari" "Zaki rufe mini baki, ko sai na kwaɗa miki mari, ni kike gaya wa ba kya saka rayuwar wani a hatsari? Duk tayar mana da hankalin da ki ke yi ba kya gani, yadda ki ke tayarwa da Abba hankali a shekarunsa ba wasa da rayuwarsa ba ce ba? To wallahi ba zaki kashe mana uba ba, muna da burin ganinsa a raye". Aikuwa ta gyara tsayuwarta, ta haɗiye wani abu mai ɗacin gaske, ƙirjinta na yi mata zafi ta ce "Good, an zo wurin, kar na kashe muku uba, tun da ni ba nawa uban bane ko? To ku mayar da ni wurin nawa uban mana, meye na zama ana yi mini gori, how many years for now? kuna yi mini gori, kai ɗin ma da baka yi yau gashi ka fara, alhalin kun fi kowa sanin bani na zaɓi hakan ba, da da yadda zan yi, da tuni na bar muku gidanku, ku nuna mini hanyar gidan nawa uban mana" Ta baya ya fizgota, ya ɗauketa da lafiyayyen mari. Gigicewa tayi, jikinta ya hau rawa ta kalli Abba, da ransa yake a ɓace, fuskarsa babu annuri. Ya riƙe hannunta, ya zazzaro mata ido ya ce "Me ki ka nema kika rasa? Me kike buƙata a rayuwar nan da ban yi miki ba da ki ke zancen mahaifinki, menene shi Nabila?" Ta sunkuyar da kai tana kuka, ta dafe kuncinta. "Ki gaya mini, kafin na kasheki, me uban naki ya tsinanawa babarki ma, balle ke? Uban me ki ke nema a wurinsa?" "Abba ka yi haƙuri, ba zan sake ba" "Ba zan yi haƙurin ba, ki gaya mini ta ina na gaza, menene ba na yi miki" Mama da jin hargowar su ya sanya ta fito ta tarar da su, ta ce "Mhmm, ai tsintacciyar mage ba ta taɓa yin mage major, kuma gurbin ido ba ido bane ba, muna nan da kai wataran sai ta saka ka zubar da hawaye" Nasir ya ƙarasa ya ce "Abba dan Allah ka yi haƙuri, ba zata sake ba in sha Allah, kar ka kuma dukanta" "Shut up! Kai ma har da kai, ina yi maka kallon mai hankali ashe ba haka ba ne, ku kuke tunzurata take wannan zancen". Ya ce "Ka yi haƙuri dai Abba, in sha Allah ba za a sake ba" Ya saki hannunta ya fice daga gidan baki ɗaya. Nabila kuwa da gudu ta ƙarasa ɗakinta tana kuka mai cin rai. *** Ƙarfe sha ɗayan dare, liti yana ƙofar gidan su Al'amin, yana rarraba ido, babu yaron da zai aika cikin gidan, kowa ya watse. Ya bubbuga gate ɗin gidan, ya koma gefe. "Waye?" "Nine" Ya buɗe gate ɗin ya kalli liti ya ce "Ya aka yi?" "Wurin Abbu nazo shi nake nema" Jin muryar liti, ya sanya Abba gane jama'ar Viper ne, dan haka ya ce "Mai zamanin yana tsare ai, ka sani kake nemansa" "Dan uwarka wurin mai zamani na ce maka na zo? Wurin mai gidan na zo, baka gane ni bane liti ne" yayi maganar yana cire facemask ɗin fuskarsa. "Na gane ka, amma a kan me zaka zo nemansa, ka gaya mini na je na gaya masa" Wata uwar shaƙa liti yayi masa, ya watso shi waje ya ce "Shege, kai ka isa in zo wurin maigida ka ce na gaya maka menene sa'anka ne ni, wallahi idan baka kiyayeni da abun da ya shafi mai zamani ba, sai na sassaraka na bar wa uwarka tabon daba, makira yar wuta" tamkar gidan ubansa, liti ya kutsa kai ya shiga gidan. Ya tsaya a tsakar gidan yana kwaɗa sallama. Rahila ce ta fito ta ce "Wane mara mutuncin ne haka a tsakar gidanmu, malam balaggagen gardi ka shigo mana gida". "Ɗanki ne ya so na shigo, eh sarkin gida nake nema, an ce ya je gada biɗata, mu kuma tsakainmu da maƙyanƙyasanmu akwai amana, mussaman maƙyanƙyashin mai zamani, ai dattijonmu ne iya wuya, ace masa gani na amsa kira". "Wace irin magana ce kake yi wannan, ni ban gane ba" "Gana ce, kuma kin gane mai nake nufi, ki yi mini magana da mai gidan, ko na shiga na neme shi da kaina" Abba ya shigo gidan yana zare ido, ya sake cewa liti "Ka zo ka fitar mana daga gida" "Gidan ubanka ne ko na mai zamani? Idan gidan ubanka ne sai na fita, idan kuma gidan uban mai zamani ne nima gidanmu ne" Rahila ta ce "Wane mai zamanin, ka tafi can ka neme shi, ka fice ka bar mana gida" "Ke yar wuta ban saka da ke ba, baƙar sheɗaniya, idan baki nemi yafiyar mai zamani ba, wuta ɗaya zaki shiga da matar sheiɗan, kai ware ka yi mini magana da mai gidan" yayi maganar yana zaro makami. Abbu kuwa bacci yake yi sosai, a cikin baccin ya jiyo muryar liti, kawai zuciyarsa ta raya masa Al'amin ne, ya zo da mutanensa. Da sauri ya fito tsakar gida, yana tambayar ko lafiya. Liti na ganin sa ya mayar da makamin, ya durƙusa ƙasa ya ce "Abbu barka da dare" "Yauwwa barka, lafiya ka shigo mana gida a wannan daren?" "Liti ne Abbu, an ce ka je namanmu, ko ni ko walid, shiyasa ban yi sanya ba, na ce bari na gangaro na amsa kira, duk da mu masu laifi ne, ya kyautu ace muna zuwa muna kawo gaisuwa" Abbu ya ce "Ikon Allah, meye sunanka na gaskiya ne?" Liti yayi murmushi ya ce "Bawan Allah nake ai sarkin gida, Abdallah ne" "To ni Abdallahn zan ce, bisimillah shigo mu shiga daga ciki" Rahila ta ce "Ya shiga ina? Makami ne fa a jikinsa, sai yayi maka illa, ya zaka shiga da shi makwancinka?" Abbu bai kulata ba ya ce "Ƙaraso Abdallah" Ya bi bayan Abbu, yana baza babbar rigar daya saka a kan ƙanan kayansa ya kalleta ya ce "Munafuka, haddsana mai raba ɗa da uba, idan baki yi wasa ba, tun a duniya sai kin tozarta" Duk tsagerancin Al'amin baya saurarta balle ya zageta, amma liti sai ƙare mata zagi yake yi. Abbu ya kalli liti ya ce "Abdallah, dan Allah ko ka san in da Al'amin yake? Tun da ya zo mini daga prison na kore shi, ban sake ganinsa ba, ina matuƙar kewarsa da son na ganshi, na san ku ne makusantan sa, ban sani ba ko kun san in da yake?" Liti ya ce "Eh to, gaskiya ban san in da yake ba, amma dai muna haɗuwa" Abbu ya ce "Ban gane ba" Liti ya ce "A bar shi hakan da na faɗa, ban san in da yake ba, amma muna haɗuwa, kuma maganar gaskiya, yana fushi da kai, tun da aka ce yayi laifin nan baka bashi dama ko sau ɗaya ba, ka saurare shi" "Wace damar zan bashi, na nema masa auren yarinya girma da arziki, amma ƙarshe yayi silar rayuwarta" Liti ya kalle shi ya ce "Haryanzu ka yadda shi ne ya kashe yar madara?" "Meyasa ba zan yadda ba, tun da ya furta mini, kuna gashi yana shaye-shaye" Liti ya jinjina kai ya ce "Haka ne" ya tashi tsaye ya ce "Baka shirya ganin sa ba, maybe zuwa gaba kaɗan, amma wallahi mai zamani, Allah ne yayi da sauran kwanansa a gaba, dan ya kusa kashe kansa, ko mun lalace fa ku iyayenmu ne, bamu da sama da ku, duk son da mai zamani yake yi maka, ka fita daga zuciyar sa, ya daina maganarka ranar da na yi masa zancenka ce mini yayi shi yanzu ba shi da uba, kaga wannan ba dai-dai bane ba, alhalin ga wani ɗan kut.... Da yafi mai kora shafawa da shi da yan uwansa, suna zaune a gidan, mu kuma kun sallamawa duniya mu. Bari na ɓace, Allah ya ƙara maka lafiya da nisan kwana, ka cigaba da yi mana addu'a a duk in da muke, mai zamani zai samu yanci ya cigaba da gudanar da rayuwarsa kamar kowa, ba tare da yana ɓuya ba" Abbu ya miƙe suka fito tsakar gida ya ce "Kayi mini wani taimako Abdallah, ka tayani kwantar masa da hankali kafin ranar da Allah zai saka na ganshi dan Allah" "To in sha Allah" Ya ɗaukko kuɗi ya bawa liti, liti ya ce "Meyasa zaka bani kuɗi, ni ba zan karɓa ba, ayi mana addu'a kawai, in sha Allah mai zamani ya kusa samun ƴanci" yana gama maganar ya fice. *** Liti ne yake ta kallon Viper, ya numfasa ya ce "Mai zamani" "Farin jakada" liti yayi dariya, ya ce "Rabon da ka gaya mini sunan nan har na manta, kwanan nan kamar kana jin raha, menene sirrin ne?" Ya ce "Abubuwa da yawa, ƙwaƙwalwa ta ta samu nutsuwa a 'yan kwanakin nan, sannan na fara jin daɗin yadda nake wasa da hankalin maƙiyana, ka san sanyawa mutum tsoro yafi kowane horo wahala" Walid ya ce "Ai mun gode Allah, da bayan tafiyar jauhar, Allah ya kawo mana Nabila rayuwar ka, haƙiƙa bayan ƴar madara ita ta ceto mana ƙwaƙwalwarka da tunaninka" "Ba wani nan, da an yi magana ka fara sako maganar wannan makirar ba wani, ba uwar da ta tsinana masa" "Wai anya liti idan aka bi salsala ba daga zuriyar fir'auna kake ba, kai wai baka yafiya ne" "Ba zan yafe ba, kace ma nine fir'aunan kawai mana walid" "A'a ni ban ce maka fir'auna ba, amma dai baka da zuciyar kirki" "Ni rabu da ni, zan yi magana ka hana ni, zaka saka na manta" Ya kalli Viper ya ce "Mai zamani, Abbu yaje rumfar sayar da shayi yana nemana ko ni ko walid" a take ɗan annurin fuskar Viper ya ɗauke. Liti ya ɗora da cewa "Na ɗan yi yawo na nemi bayanai, kar na je ko wani set up ne, amma na fuskanci lafiya ƙalau ne, dan sai na ci uwar agolan nan na gidanku, da ya kawo mini wargi, mun haɗu da Abbu, ya ce mini yana son ya ganka, amma na ce ban san in da kake ba, akwai tarin nadama a tare da shi, dan Allah mai zamani ka sassauta, naka mahaifin ne kawai ya rage mana, mu yi haƙuri mu yafe masa, na tabattar masa da ka kusa yin 'yanci da yardar Allah" "Bani da uba, nawa uban ma mun rasa shi, dama can ba ya ta tamu, dukkanmu marayu ne, da muke zaune a matsayin ƴan uwan juna, ko na yi ƴanci, ba zan sake zuwa in da yake ba, na bar shi da waɗanda yake so" "A'a Viper, su fa iyaye komai za su yi, ba a fushi da su" harshensa ya zaro waje, ya ɗago sweazland ɗin da take gefensa, ba shiri liti ya tsuke bakinsa, yayi shiru ba dan ya rasa abun faɗa ba, sai dan sanin cewa yana sake magana sai ya saka masa ƙarfe. Message ne ya shigo wayar Viper. "An yi maka gargaɗi a kan yarinyar nan tun da farko, amma ka ƙi ji, yanzu ta zama rauninka, sai ka yi aiki tuƙuru, dan kare rayuwarta!. *** Nabila ba ta san ya aka yi aka samu lambar wayarta ba, mutane suka din ga kiranta a waya, wasu na zaginta a kan program ɗin da ta gabatar, ta taɓa bunkure foundation, wasu na jinjina mata, tare da nuna mata goyon bayansu, da ta gaji kashe wayar ta yi gaba ɗaya. Gaba ɗaya kewa da tunanin Viper, suka haɗu suka uzzurawa rayuwarta, tana ta ƙoƙarin basarwa amma abu yaya gagara kamar yadda dariya ta gagari kare. Ta tsaya a gaban mudubi tan ƙarewa kanta kallo, bayan ta fito daga wanka, ta shiga ƙarewa kanta kallo, kyakykyawar farar fatarta sai sheƙi take yi. Idanunta jawur, saboda kuka, gaba ɗaya haushin Nasir take ji, gaba ɗaya komai yayi mata zafi, ba ta jin daɗin komai. Message ne ya shigo ƙaramar wayarta, "Mu haɗu a garden" ta zubawa notification ɗin ido, tayi wata irin ajiyar zuciya, kamar sanyi ta ji a ranta, da ganin saƙon nasa. 'Wai me nake yi haka ne? Ta tabatta son shi nake yi kenan? Wace irin ƙaddara ce haka?" Ta lumshe idanunta, hawaye ya ziraro daga idaunta, abubuwa da yawa suna damunta, kuma babu wanda take burin ta gayawa sama da Al'amin, mutumin da bai damu da ita ba ko kaɗan. Jiki a sanyaye ta shirya, ta saka kayanta, ta kawo facemask ta saka, ta fice. Ko da ta je garden ɗin, ba ta tarar da shi ba, ta kira wayarsa amma ba ta shiga, haushi ya kamata, ranta ya ɓaci, dan da niyyar ta ganshi ta zo, haka kurum tayi ta ɗokin ta zo su haɗu. Ta nemi wuri ta zauna cikin takaici, haushin kanta take ji, yadda ta faɗa soyayya cike da wawanci. Ta ɗan jima a wurin a zaune, sannan ta tashi, ta ɗauki mota zata koma gida, ya kirata a waya. Bai jira tayi magana ba, ya fara "Yayanki yana bin bayanki, nan da kilometer biyu, akwai wani gidan cin abinci, ki tsaya ki shiga" ya gama maganar ya katse. Babu tunanin komai ko musu, ta cigaba da tafiya, sai dai ta din ga kallon mirror, amma bata ga alamar wani ita yake bi ba. Ta tsaya a restaurant ɗin, ta shiga ta sake kiran wayarsa, bai ɗaga ba ya tura mata saƙo "In the next 10 minutes, ki koma motarki, ki samu wuri ki zauna ki jira" "Wai dan Allah meyasa...... Katse wayar yayi, ba tare da ta gama maganar ba. Ta nemi wuri ta zauna ranta a ɓace, mintuna goma na cika ta ga saƙonsa. Ta tashi ta fita, ta ƙarewa harabar wurin kallo, amma ba ta ganshi ba, ta buɗe motar sai da ta zauna, kawai ta ganshi a cikin motar, da ihu zata kurma, amma tayi shiru, tana rarraba ido, ta rufe motar ta kalleshi ta ce "Ta ina ka shigo?" "Ta ƙofa" ya bata amsa. "Amma to meyasa kayi ta wahalar da ni?" "Fita ki zagayo, zan ja motar" ta jinjina masa kai, ta fita ta zagaya, shi kuma ya koma mazaunin direba, ya bawa motar wuta, ya ja ta da uban gudu ya bar wurin. "Ka tuƙa a hankali, tsoro nake ji" bai ce mata uffan ba, ya cigaba da fafara gudu, sai da ya cimma wani a kan babur, ya sanya hular kwano. "Kin san wannan?" Ta girgiza kai alamar a'a. "Kin tabatta?" "Eh, ɗazu dai ka na ƙaraso nan, na wuce shi a kan titi" Ya jinjina kai ya ce "Ke yake bi, kin wuce ni a mota, na ga yana binki, ina kyautata zaton ko dai yayanki, ko wani ne ya sa ya din ga binki" Ta sauke numfashi ta jingina da jikin dai-dai lokacin da ya saka hannu a jikin seat ɗin, yana ƙoƙarin shiga wata kwana. Tudun gashinta ta ɗor a kan hannunsa, ta lumshe ido, fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa, jikinsa ne yayi wani irin sanyi, yayi saurin cire hannunsa, ya ƙarasa in da yake son su je. Shi ma lambu ne wurin, amma babu kowa, sai sanyin bishiyun wurin, ta fuskanci yana son yanayi irin haka. "Yaya ake ciki da case ɗin rahama, a ina ki ka tsaya?" Kawai ta zuba masa ido, ya yi mata wani irin kyau, ma'abocin ƙanan kaya ne, shirt ce ajikinsa baƙa da zanen damusa a jiki, sai dogon wandon jeans, mamaki ma take yi, a in da yake samun kuɗin sayen kaya masu kyau. Sai ƙamashin turaren florie yake yi, ya yi gyaran fuska, ya kuma yi saisaye, idanunsa sun rage wannan jan, alamu sun nuna ya ɗan tsagaita da shan miyagun ƙwayoyi. "Malama ina magana kin yi shiru kina kallona" "Yanzu rashin muhimmancina har ya kai na shiga wannan tashin hankalin, ka sani amma ka kasa nema na ko a waya, ka ce mini sannu, i almost lose my life fa, a yaya ka ɗauke ni ne? Bani da muhimmanci har haka a wurinka, haba dear, ni ka san ba zan taɓa yi maka haka ba, ina son rayuwarka, ina son ganin walwalarka da farincikin ka, ina son na maye maka gurbin jauhar, da wasa na ɗauki abun, amma ya zame mini gaske. Ka daina nuna mini halin ko in kula, bana jin daɗi ko kaɗan. Damuwa ce da ni a raina sosai, ina son wanda zan gaya wa ya saurare ni, wanda zai fahimci haƙiƙanin abun da nake ji" "Ki shiga hankalinki, bana son wannan wasan da ki ke yi mini, da zarar aikina da ke ya kammala, kowa zai kama gabansa, ki daina yi mini irin wannan wasan, na gaji da yi miki kawaici, ba na so" Cikin ƙarfin halin da rauninta ya hana ta aikata hakan, hawaye ya fara biyo kuncinta ta ce "Ba wasa nake yi maka ba, ƙaddara ce da na roƙawa kaina da bakina, ba wasa nake yi maka ba, da fari wasa nake yi, amma yanzu ya zame mini gaske, ban taɓa tunanin zan iya cewa wani namiji ina son shi ba, amma kai naga kamar nutsuwar ka ta kai na gaya maka" Ya ce "A'a karki yaudari kanki, wace nutsuwa nake da ita?" "Rauninka mutane kawai ke iya gani, ni kuma nagartarka nake gani, kamar kai ne zaka zama dai-dai da ƙaddarata" Wani abu ya ji yana nema ya rinjayi zuciyarsa, mussman da ya fara ganin fuskar jauhar a cikin ta Nabila tana kuka. Cikin ƙarfin hali, yayi ta'awizi ya kaurara muryarsa cikin tsare gida ya ce "Jauhar ɗaya ce, kuma na sameta ta suɓuce mini, babu wata mace da zata iya maye mini gurbinta, sanya wata macen a zuciyata tamkar cin amanar 'yar madara ne, a kanta na gama soyyaya, kuma na gama aure, dan haka kar ki ƙara yi mini wannan maganar, ki nemi wani ki aura, wanda iyayenki za su yi alfahari da ke da shi, jauhar ma ƙaddara ce ta saka aka bani ita" Ta share hawayenta ta ce "Nabila mace ce mai aji, aji ma na gaske, ban taɓa mafarkin fara furtawa wani namiji ina son shi ba, raunin macen kenan, daga tausayi na faɗa sonka ban shirya ba, kai banda ƙaddara da haɗin Allah, me zai kai mace kamata yin kasada da rayuwata kamar wata wawuya ina nemanka ina zaman zamana?. Sannan ka sani idan akwai macen da nagartarta zai hana a auri wata mace bayan wafatinta, to Sayyada Khadijah ce Allah ya ƙara mata yadda, kuma idan akwai macen da soyyayar da ake yi mata, zai hana ayi mata abokiyar zama, to sayyada Aisha ce radiyallahu anha. Baka san wace damuwar ce a raina ba, ka zaɓi ka yi mini haka, ko baka so na, ba haka yakamata ka yi mini ba, bani mukullin motata na tafi" tayi maganar tana kuka tare da miƙa masa hannu. Kallonta kawai yake yi, babu in da ta bar 'yar madara a kamanni, hatta kukan nan da take yi, jauhar kawai yake gani, sai dai Nabila ta fi jauhar murya, da kilewa kuma ita mafaɗaciya ce. Loosing control ɗin sa ya kusa yi, da zuciyar sa take raya masa, ya rungumeta ya rarrasheta, sannan ya ji menene damuwarta, fizge mukullin motar tayi, ta ƙara gaba tana kuka. Ayshercool 08081012143 67 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin zafin nama ta juya tana kuka, ta nufi hanyar barin wurin, har ya ɗaga ƙafa da niyyar ya bi ta, sai kuma ya fasa, dan idan ya bita bai san me zai ce mata ba, yana kallonta ta hau motarta ta bar wurin. Bashi da zaɓin da ya wuce shi ma ya bar wurin, sai dai ya tafi zuciyarsa cike da wasi-wasi, ko cikin duhu aka tara mata dubu, zai cire 'yar madararsa, amma haryanzu ya kasa gane dalilin da ya sanya Nabila take kama da jauhar, ba kuma wai kama sama-sama baz kamannin ne tamkar an raba kara biyu. Ya cigaba da takawa a hankali ya bar wurin. *** "Indabo ina fatan ka saurari program ɗin da wannan sheɗanun yaran suka gabatar, ka shirya ɗaukar mataki ne, ko kuma ni na ɗauka da kaina? Na gaya maka ba zan bari wahalata ta shekaru ta tafi a banza ba, in ƙare a lalace, ƙaramar yarinya ta rusa ni ba, ko dai ka saka a dakatar da program ɗin nan, ayi abun da ya dace a kanta, ko kuma ni zan ɗauki matakin abun da ya dace" Indabo ya kalleta ya ce "Naja, wai yaushe ki ka zama haka ne? Duk wata matsala tare muke magance ta, amma wannan sai nema ki ke yi ki zame, ba fa wata babbar matsala bace ba" "A wurinka ne ba babbar matsala ba, kuma ƙaramar matsala ita ce take zama babba. Kana jin manyan lauyoyin nan da basu samu dama a kaina ba da, yanzu sun samu suna ta bata goyon baya, mutane sun fara farga da abun da take yi, ni na rasa wai waye uban ɗakinta ne waye ya tsaya mata?" Ya numfasa ya ce "Kankarofi ne" "What? Kankarofi kuma? Meya kawo shi cikin wannan maganar?" "So yake lallai sai ya ga bayana, ya rama abun da ya faru a baya, maimakon ya rama a siyasance, ba ta haka yake son yi ba, so yake lallai sai na tozarta" Naja ta ce "Ikon Allah, to menene ribarsa, alhalin kuna sirikai?" "Aurenma da ya auri jidda, duk cikin plan ne na siyasa, kin san ita siyasa babu maƙiyi na dindindin, kuma babu masoyi na dindindin, mun zauna jam'iyya ɗaya da shi a baya kamar yadda na taɓa gaya miki. A lokacin nan mutane suna matuƙar sonsa, duk da ba wani babba bane ba, kuma naga take-taken ana kiransa ya fito takarar kujerar da nake hari. Na shiga na fita da wasu mutane, sai da suka fita suka bar mana jam'iyyar, duk da a lokacin ba wani mayar da hankali yake a kan siyasar sosai ba, gidansu yan kasuwa ne, shi ne yake taɓa siyasa. Bayan sun bar jam'iyyar, aka bani takara, shi ma jam'iyyar da ya koma, suka bashi takara, nayi ta bita da ƙullin siyasa, da yi masa yarfe kala-kala. Ni da yan jam'iyyar mu, kasancewar muke da mulki a sama, muka shiga muka fita, aka murɗe zaɓen, ya ce shi ba zai kai ƙara ba, jam'iyyarsa suka kai ƙara, amma duk aka kori ƙarar, duk da haka mutane suka so yi mini bore, shi suke so. Na haɗa kai da shugabannin jam'iyyarmu, muka kunno masa wuta ta sama, EFCC suka zo har gida suka kama shi, aka yi seazing ɗin wasu kadarorinsa, da zimmar ya mallake su ba bisa ƙa'ida ba. Kasancewar ba shi da manyan iyayen gida, bai iya shige-shige da neman wurin zama da biyayya a wurin manya na wannan lokacin ba, ya sanya sai da aka tsare shi a prison, ana binciken sa, bayan an sake shi duk da haka aka ƙwace masa kadarori. A lokacin mahaifinsa ya ce, baya son sa da harkar siyasa, ko zai yi ya bari sai bayan ransa, sai ya cigaba da kasuwancinsa, kuma bai taɓa ce mini uffan ba, sai bayan rasuwar mahaifinsa ya dawo yake taɓa harkar siyasa, har aka yi masa muƙamin nan, ashe ya ƙwafe wannan abun a ransa, so yake sai ya ɗauki fansa ta ƙarfin tsiya yanzu" Naja ta ce "Taɓ, gaskiya kana ruwa indabo" "Ban gane ina ruwa ba?" "Au muna ruwa zan ce? Wannan rigimar ai ban san lokacin da aka yi ta ba, balle ace da ni aka ƙulla a nemi mafita, a kanka yake neman fansarsa, dan haka ni kar a saka ni a ciki ba zai yiwu ba, haka kurum ana nema ayi mini tsirara a idon duniya" "Naja" "Na'am" "Haka ki ka ce? Kin san bana tafiya da butulu?" "Babu in da nayi maka butulci, na bauta maka da ƙarfina da gangar jikina, abun da nake yi ba butulci bane, iya ruwa ne fidda kai" Ya jinjina kai ya ce, "Haka ne, na fahimta" *** Abdul ne a zaune, ya zubawa ramma ido, tamkar mahaukaciya, gaba ɗaya ta burkice masa, idanunta sun yi jawur saboda kuka, yana kallonta rabonta da abinci tun jiya, muryarta duk ta dashe saboda kuka, ya ma rasa ya zai yi mata, yayi tsawar ya zare idon, amma duk a banza. Ya kaɗa ya raya taƙi cin abinci. "Rahama" ta ɗago ta kalleshi kamar wata dodanniya. "Me ki ke so?" "Ka duba ni, wallahi ba zan zauna da cikin shege ba, idan shi ne ka cire mini, ka mayar da ni gaban uwata, na gaji da yi maka biyayya baka da niyyar cika alƙawarin da kayi mini, ban sani ba ko sai ka cika alƙawarin ka na kasheni sannan hankalinka zai kwanta". "Yanzu da kanki ki ke cewa a zubar da ciki? Alhalin lokacin da tsautsayin nan ya faru, mun nemi a zubar a rufe maganar amma ku ka ƙi" Kamar ta ɗura masa ashar ta ce "Wancan idan tsautsayi ne wannan fa? Wallahi Abdul zan kashe kaina in huta, na gaji" Ya ce "Is ok, shikenan yanzu ko cikin ne babu lallai na gani, ki bari zan tafi da ke asibiti na yi miki gwaje-gwaje sosai, amma sai kin yadda kin yi wanka kin ci abinci" Cikin rashin wayo ta jinjina kai, ya lallaɓata da kyar, ta yi wanka, ya dafa tea da indomie ya bata, sai dai tana gama ci, ta hau amai. Ya ce "Kin gani, ulcer ta kama ki, daga jiya zuwa yau da baki ci abinci ba, shiyasa kina cin abincin ki ka yi amai" Cikin kuka ramma ta ce "Wallahi ciki ne da ni, ni bani da wata ulcer " "In ji wa? Ulcer ai tana saka amai, baki ga nima yadda take yi mini ba ne? Ai rashin cin abincin ne ya janyo haka, kuma idan ki ka cigaba da ƙin cin abincin tumbinki ne zai ta rarakewa, komai ki ka ci sai kin yi amai". "Dan Allah da gaske kake, ulcer ba ciki ba?" "Zan yi miki ƙarya ne?" Yayi maganar yana tsuke fuska. "To ka rantse da Allah" "Ba zan rantse ba, ina likita zan yi miki ƙarya ne? Kuma kan nayi miki allura ban gaya miki allurar tsarin iyali na iya ɗauke miki al'ada ba, tun da artificial homones ne aka saka a jikinki ba?" Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Eh ka gaya mini" "Amma shi ne ki ke ta yi mini wannan borin ko rahama, ni ko?" "Da ka san me nake ji a zuciyata da baka ce ina yi maka bori ba, na gaya maka mamana mu biyu ne da ita, yayanmu ma ya mutu, ya za ayi hankalinta ya kwanta ina nan? Kalli tsawon lokacin da na ɗauka ban ganta ba, ka tausaya mini mana" Ya saka hannu yana share mata hawaye ya ce "Zan mayar da ke rahama, sonake sai na sanar da mahaifina komai tukuna, bana son sunanki ya ɓaci kamar yadda ki ke ta iƙrari" "Ɓacin suna na nawa kuma? Ai ya riga ya ɓaci" "Zan gyara shi da yardar Allah babyna" Sai da yayi ajiyar zuciya da yaga ta ɗan nutsu har ta ɗan saduda, sai da ta samu bacci, sannan ya tashi ya fita, ya kira saif a waya ya ce masa su haɗu. *** A harabar gida Nabila ta tarar da Nasir, tana gama parking ya fito daga cikin tasa motar ya tareta ya ce "Daga ina ki ke?" Kamar ta wanka masa mari, a hasale ta kalleshi ta yi shiru. "Ina magana kin tsare ni da ido" "Iska na fita sha" "Wa ki ka gaya wa, sai Abba ya dawo yayi ta faɗa ko? Kuma wace irin shan iska ne zaki fita ki yi nisa da gida, kukan me ki ke yi ma?" "Dan girman Allah ka ƙyale ni" tayi maganar cikin sauti mai ƙarfi, ta nufi cikin gida da sauri, kamar mahaukaciya sabon kamu. Ta shiga ɗakinta, ta rufe ƙofa ta wulwula jakar hannunta tayi jifa da ita, ta samu wuri ta zauna ta dafe kanta, da take jin tamkar zai rabe biyu. "Ya haiyyu ya ƙaiyyum, ya zuljalalu wal ikram" take ta maimaitawa, tunanin ma ta rasa wanne yakamata ta yi. Viper ya ƙular da ita, amma tafi jin haushin kanta, da ta iya buɗe baki, ta furta tana son shi, a da ko me za ayi mata, ko da wasa ba ta taɓa sakawa a ranta zata iya furtawa wani tana son shi ba. To saurayi ya ce yana sonta ma, wahalar da shi take yi, ko da tana sonsa, saboda ta ja ajinta, amma wai yau ita ta furtawa wani so, kuma yayi rejecting ɗin ta kai tsaye. Viper yana da qualities ɗin da ya cancanci a so shi,  ba ta taɓa zaton wasan da take yi zai zama gaskiya ba, dan ita da fari tsokanarsa kawai take yi, sai kuma matsanancin tausayin sa sa take ji, gashi tausayi ya juye ya koma mata soyayya shi kuma baya ta tata, ga wannan tsohon ciwon nata da ta fama. Zuwa yaushe Abba zai fuskanci gurbin ido ba ido bane ba, duk wani abu da ya faru a baya, bata san an yi shi ba, ba ta san maman nata ba dama wannan an tabattar mata da bata raye, to mahaifinta fa, komai lalacewarsa zata so ta ga abun ta, kuma komai ya yi wa mahaifiyarta, wani abu ne da ya wuce a baya, da ba ta nan ma aka yi shi, to na menene za a gadar mata da wani abu da ba shi da tushe balle cikakkiyar makama. Ta zabura ta tashi, ta watso drower littatafanta, ta ɗaukko hotunan mahaifiyarta, cikakkiyar bafulatanar yarinya ce ba wata babba ba, fara sol da ita mai dogon hanci, tayi ɗauri irin na mutanen da, ta zubo da dogon gashinta ta ƙarƙashin ɗan kwalinta, har ka kafaɗarta, dukkanin hotunan uku, fuskarta ɗauke da murmushi daga yanayin hotunan zaka fahimci ba ta da hayaniya, kuma mai yawan murmushi ce. Ta daɗe tana kallon hotunan tana kuka, ta gaji ta kwanta a kan gado, sai ajiyar zuciya take yi. Washegari da safe, ta shirya zata tafi wurin aiki, ta shiga wurin Abba ta gaishe shi, amma ya shareta yaƙi amsawa, sai gajiya tayi, ta tashi ta fita. Ko da taje wurin aikin ma, kanta ta kifa a kan teburin office ɗin ta. Barrister Habib har yayi knocking ya shigo, ba ta sani ba, sai da ya daki teburin, sannan ta ɗago. "Nabila ya dai? Na ji program ɗin ki ya ɗau hankalin mutane, ki zo a mayar da hankali wurin neman shaidu, kin shigo kuma kin zo nan kina bacci" Tayi shiru ba ta ce Komai ba. "Wai meyafaru ne?" "Ba na jin daɗi ne" "Yasalam, sannu kuma kika fito? Kina da tiral ne yau?" "A'a, na zo ne dama mu cigaba da aikin shari'ar nan, ai na sha magani, bari na biyoka office ɗin" Tare suke aikin, amma sam hankalinta baya kan aikin, ƙarshe ya ce, su bari sai ta samu sauƙi tukuna. *** A wani wurin cin abinci saifu suka haɗu da Abdul, suka zaune saifu ya ce "Mutumina harkar siyasar nan duk ta ɓoye mana kai, wurin chilling ɗin ma duk ka daina zuwa. Hafsa ta ce tana son ta zo ta ganka, na ce ko ta je asibiti baka zama, ayyuka sun yi maka yawa, asibitin ma ba wani zama kake yi ba" Yayi murmushin ƙarfin hali ya ce "Ya jikin nata?" "Da sauƙi sosai Alhamdilillah, likitanta ma sun sallameta, sun ce ta warke, ina ga wani abun ne yake damunta, ta ce kafi dubata sosai, na rasa wani siddabarun kake yi wa patient suke liƙe maka" "Saif, mu bar wannan maganar, akwai damuwa fa" "Ta me?" "Haryanzu babu labarin mahaifiyar yarinyar nan, gashi kuma ta matsa mini, kullum cikin kuka take" Saifu ya ce "Ai fa Abdul ka yi mugun ganganci abun da ka aikata, ka mayar da ita wurin iyayenta, tun kafin asirinka ya tonu, sunanka ya ɓaci" "Saif, ni fa ba ta sunana ya ɓaci nake yi ko akasin haka ba, ni wallahi burina kawai na cigaba da ratuwata da ita, wani irin abu nake ji a kanta, da rabani da ita tamkar rabani da rayuwata ne" "Kai Abdul, ba ka gama ɗibar abun da kake so ba, ko haryanzu bai isheka ba?" "Ba wannan nake yi wa ba, ita nake so, tun bayan da na ɗaukota take bani tausayi, ka san ban taɓa raping ba, sai a kanta, wallahi son rahama nake yi, so mai tsanani". Cikin mamaki Abdul ya ce "Taɓɗijan, aurenka ne fa yake gabatowa, yanzu yaya kenan, gashi ana ta fitina a kan ainihin wanda ya yi mata fyaɗen, wata lauya ta kafe, sai an fito da ita ta bayar da shaida a kotu. Ina ga fa dolenka ka gaya wa mahaifinka gaskiya, ya ɗauki matakin da yakamata a rufe abun nan". "Ina son gaya masa, amma ina tsoron abun da zai iya yi, ba zai ɗauki maganar da sauƙi ba" "To ai kuwa ko da yaya zai ɗauki maganar, haka ne kawai mafitar" Abdul ya yi shiru yana zancen zuci. *** Viper yana zaune, ya tsurawa hoton jauhar ido, yana hararo kamannin Nabila a cikin kansa. Walid ya dafa shi, ya ɗaga kai ya kalle shi. "Ya ake ciki ne? Mutuniyar kwana biyu, yakamata ace fa shirye-shirye sun yi nisa a kan shari'ar ka, ta ina za a fara?" Viper ya ce "Fushi take yi " Walid ya ce "Fushin me? Wani abun ya faru ne?" Ya girgiza kai ya ce "Akwai magana a bakinta da yakamata na saurara, wataƙila zai haska mini abun da kake gaya mini, sai dai ta bijiro da abun da dole na taka mata burki" "Wane abu ne?" Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Bakomai" "Mai zamani, yakamata ka din ga bin komai a sannu, mata fa dukkansu ba irin jauhar bane, jauhar one in million ce, ba kowace mace ce zata iya juriyar da ta yi ba, kar ka yi treating ɗin Nabila yadda kake treating ɗin Jauhar, suna da banbanci" Yayi shiru, ya cigaba da kallon hoton hannunsa. "Allah ya jaddada rahama a gareki, ya kyautata makwancinki my wife " yayi maganar yana shafa haƙoranta na jikin hoton da yake da shi da ita ne, fuskarsa da ƙuruciya sosai lokacin. Walid ya ce "Amin" ya karɓe hoton, ya ajiye shi a wani wurin. Yayi shiru yana tunanin ko me Nabila take son ta gaya masa? Ko yanzu tana wani hali? Da gaske son shi take yi, ko kuwa dai still da wasa take yi? Kukan da tayi ya tabattar mata ba wasa take yi ba. To su mata babu wuya sun fara son mutum kenan? Ya ga damuwa sosai da sosai a cikin idanunta da suka haɗu, ya so ya ji menene damuwarta, amma ta zo da lamari mai girman gaske, son da take yi masa wahalar da kanta kawai zata yi, yana cikin wannan halin na ɓoye-ɓoye, idan ta fara son shi yaya zata yi, tun da ba aurenta zai yi ba, kuma shi ba ma wannan ne a gabansa ba gaba ɗaya. *** Kusan kwanaki huɗu, amma Abba baya saurar Nabila, fushi yake yi da ita sosai, gajiya tayi da fushin da yake yi da ita, ga habaici da yar da magana da ake yi mata a gidan. Ta shirya tafiya aiki, ta shiga ɗakinsa, ya na karyawa. "Abba ina kwana" yayi mata shiru ya cigaba da karyawa. Ta tashi ta je gabansa ta zauna cikin kuka ta ce "Dan Allah Abba ka yi haƙuri ka yafe mini, dan Allah ka yi haƙuri ka yafe mini, in sha Allah ba zan sake maganar babana ba, idan raina ne ya ɓaci aka yi mini gori, duk sai na ji babu daɗi amma dan Allah ka yi haƙuri ka yafe mini ba zan sake ba" da fari yayi mata shiru, amma daga baya ya numfasa ya shafa kanta ya ce "Kukan ya isa haka, na ji na yafe miki, duk da kin sha yi mini wannan alƙawarin amma ba kya cikawa, yau da mahaifinki wani abun kirki ya tsinanawa mahaifiyarki, rabuwar arziki aka yi, babu yadda za ayi na nesanta ki da shi har haka, na yanke duk wata alaƙa tsakaninki da shi. Ki yi haƙuri na san kina haƙuri da abun da ake yi miki, da zarar kin yi aure shikenan kin wuce wurin, ki yi haƙuri ki cire maganar mahaifinki a zuciyarki" Nabila ta jinjina kai, amma ƙasan zuciyarta ba ta ji zata iya daina maganar mahaifinta ba. Ta tashi ta fita ta tafi aiki, ita ma ta fita daga harkar Nasir gaba ɗaya. Yau ba ta da shari'ar da zata halatta, dan haka tana office tana ta nazarin shaidunta, da za su yi appeal. Wayarta ce tayi vibrating, ta ɗaga ta duba "Mu haɗu a restaurant ɗin da ki ka je, zamu yi magana mai muhimmanci" ta zubawa wayar ido tana kallonta, ta ajiye wayar. Har mamakin kanta take yi, yadda take abu babu tsoro take wannan kasadar haka. Ta ajiye wayar ta kifa kanta, can ta miƙe, ta tattara system ɗin ta da kayanta, ta tashi ta fito, suka yi karo da barrister Habib. Ya ce "Yauwwa wurinki zan zo dama, ina son mu je unguwar da abun nan ya faru ne, ko da wani abu da zamu kuma samu, da bamu haske a kan shari'ar" Ta ce "Amm ganin likita zan je ne, ko mu bari sai gobe in Allah ya kaimu?" Ya ce "Subhanallah, jikin ne dai?" "A'a ba wani abun damuwa ne sosai ba, zan dai je na ga likita ne, yau yakamata na koma dama" "Ok, to Allah ya ƙara afuwa" Ta amsa da Amin. Ta je wurin cin abincin, ta kira wayarsa ya ɗaga. "Gani na zo ina wurin" "Ki miƙe sosai ciki, ki tambayi Vip 2" ta ƙarasa ta tambaya, aka nuna mata, ta buɗe ta shiga. Yana zaune, ya ɗora ƙafafuwansa a kan tebur, yana sanye da facemask da facing cap ya rufe fuskarsa. Fuskarta babu annuri, ta ƙarasa ta ja kujera ta zauna, ta ajiye jakarta da wayarta, da mukullin motarta, amma ba ta ce komai ba. A yanayin yadda ta tafi wancan karon, bai zaci da ya ce ta zo zata kuma zuwa ba. Tayi masa shiru, tana danna ƙaramar wayarta. Ya ɗan daki teburin ya ce "Attention, magana zamu yi" Ta ajiye wayar ta ce "Ina ji" Ya ja babbar wayarta, ya buɗe ya ɗaukko tab ɗin sa, ya fara daddanawa. Mai kawo abinci yayi knocking, ya kawo ruwa da lemo. Ya sauke facemask ɗin sa ya ce "Yaya ake ciki da maganar wancan case ɗin, zuwa yaushe zaku yi appeal ɗin? Sonake ki kammala da wancan shari'ar, sannan ki mayar da hankali a kan tawa, already ina da shaidu guda biyu a ƙasa" har yayi maganar ya gama, bata ɗago ta kalleshi ba, wasa kawai take yi da zobunan hannunta. "Magana fa nake yi" "Ina ji ai" "Ba jin nake buƙata ba, hankalinki zaki bani" iya idanunta ta ɗaga ta kalleshi tana yi masa wani irin kallo. "Ina magana a kan yaushe zaki yi appeal, ki zo ki fara processing tawa, ina da shaidu biyu a ƙasa" still ba ta ce komai ba ta cigaba da kallonsa. Zubawa sarautar Allah ido yayi, ya saka mata nasa idon shi ma, ta gyara zamanta, ta kwantar da hannunta a kan teburin, ta ɗora kanta ta kwanta ta yi masa shiru. Ƙasa yayi da muryarsa ya ɗan matsa ya ce "Meyake damunki ne?" Kawai ta fashe da kuka, yayi mata shiru, tayi iya yin ta, ta ɗago ta share hawayenta ta ɗauki jakarta, ta ɗauke wayarta daga gabansa, ta juya za ta fita. "Ina miki magana zaki tafi? Ina zaki je ina yi miki magana?" Yayi maganar cikin tsawa da sai da ta firgita, ta ja da baya tana kuka. "Talk" yana mata tsawa tana ƙara sautin kukan nata. "Meyake damunki? Kin san haka zaki yi mini, ki ka yi mini tayin dawowa normal rayuwata? Ki ka ce zaki taimaka mini" "Ina amfanin tarayya da mutumin da kansa kawai ya sani kuma yake so? Ba cewa kai baka so na ba? Rashin amsa tayina bai yi mini ciwo ba, irin halin ko in kula da ka nu na wa rayuwata, hakan na nufin duk da risk ɗin da na saka rayuwata baka damu ba ko da zan rasa rayuwata. Saboda kana ganina a haka do you know what am going through ne? To an fasa taimakon naka, i destroy the deal and i am out of it, ka je kayi duk abun da ka ga dama" Murmushi ya yi, sai da haƙoransa suka fito, abun da ba ta taɓa gani ba. "Angry bird, always angry for no reason, duk saboda na ce bana sonki, ki ke wannan abun? Ba zan taɓa sonki ba, zuciyata ta jauhar ce itakaɗai" "Ai baka burgeni ba, da aka zauna baka bi ta lahira ba" Viper ya ce "Ai nayi niyyar bin nata, ki ka hanani, wannan deal ɗin sai an kai ƙarshensa da ke" "Komai zaka yi, ba zan sake zuwa in da kake in dai ni yar halak ce, babu amfani tarayya da mutumin da kansa kawai ya sani" ta raɓa shi ta wuce ta bar wurin. Ajiyar zuciya yayi, ya koma ciki ya zauna. Gida ta tafi, abun duniya duk ya dameta, tana ganin kiran sumayya, amma ta share ba ta ɗagawa, gaba ɗaya ta zama so silent. *** Abdul ne yake kallon ramma, yadda take ya shiri, ya ce wai shirin me ki ke yi haka ne? "Asibitin ka zaka tafi da ni, ni dai mu je ka duba ni na tabattar" "Rahama haryanzu tunaniki ƙarya nake yi kenan?" "To wa ya sani, tun da haryanzu ban ji na warke ba, amai yaƙi tsayawa, muje idan ma shi ne kawai ka zubar da shi" Ya girgiza kai ya ce "A'a ni ba na zubar da ciki gaskiya" Ta kalleshi sheƙeƙe ta ce "Yaushe ka fara tsoron Allah, har ka ke cewa ba ka zubar da ciki?" "Ai lokacin da zan kama aiki, rantsuwa nayi, ba zan ci amanar aikina ba" "Kai har wata darajar rantsuwa ka sani? Ni ka daina yi mini wasan kwaikwayon nan, kawai mu tafi" "Rahama mutuwa fa aka yi a wurin zubar da cikin nan" "Na ji, bakomai, Allah ya yi mini rahama". Ya sauke numfashi ya ce "Na ji, zamu je, amma wallahi ki ka takura mini ba zamu je ba, kuma kar ki dame ni" Ta haɗe rai ta ce "Zan baka nan da sati ɗaya, idan na ji shiru zan kuma magana" ta cire mayafinta, ta bar ɗakin. *** Unguwar gidan aikin ramma take son sake zuwa, kamar yadda barrister Habib ya buƙata, take ta yi masa yawo da hankali. Tana daf da shiga mota, ta tsaya tana amsa kiran waya. "Salamu alaikum, Barrister, walid ne" Ta ce "Oga walid, ya kake?" "Lafiya ƙalau, mutumin ne babu lafiya fa, ko zamu haɗu a wani wurin mu kai shi asibiti a motarki, saboda yanayin tsaro" Gabanta ya faɗi ta ce "Subhanallah, wani abun ya je ya sha?" "A'a, ai rabon da ya sha wani abu, an kwana biyu, ciwon ciki yake yi, tun yana yi sama-sama, tsakanin jiya da yau har suma yake yi" A rikice ta ce "Ya salam, a ina zamu haɗu to? Ina wurin aiki gani nan" Da gudu gudu, ta ƙarasa ta hau motar, ta ja, tana tafe tana waya da su, har suka haɗu, sun ɗaukko shi a adaidaita sahu. A sume suka saka shi a motarta, hankalinta yayi mummunan tashi ta ce "Oga walid yana numfashi?" "Eh yana yi, Suma dai yake ta yi" "Yanzu wane asibitin zamu nufa? Ka ga wancan ga matsalar da aka samu" Suka tattauna suka yanke shawarar kai shi wani asibitin daban. Asibitin shi ma a wajen gari yake, amma yayi kyau ya tsaru, ko ina tsab da shi. Nan da nan aka shiga da shi emergency, aka fara yi musu tambayoyi a kan meyasame shi. Su walid suka yi musu bayani, aka tafi da shi wurin yin scanic. Nabila ta fita da sauri, dan ta je ta ji ya tsarin Asibitin yake, da biyan kuɗin, taga ɗan mama yana ƙoƙarin komawa in da ya baro su. Ta ce "Sannu ɗan mama" Ya ce "Yauwwa, an gano meyake damun nasa?" Tayi murmushi ta ce "Suna ƙoƙarin yin hakan dai, wannan karon ma ka je ka sanar da su ne su zo su biya bills ɗin asibitin nasa?" Yayi turus yana kallonta, ya ce "Kamar yaya?" "Kamar yadda wancan karon kayi, kai ka yi waya aka biya bill ɗin Viper, dan babu wanda ya san mun je asibiti, yanke muka din ga yi, mu ƙaddara ma wani ya sani yana bibiyarmu, ana tsaka da treating ɗin sa hankalinmu yana kansa, ka zame ka fice. Kana kawo masa miyagun ƙwayoyi a duk lokacin da ya buƙata, abubuwa da yawa idan ba na kusa da shi ba babu yadda za ayi a san su, wa ka ke yi wa aiki?" Ayshercool 08081012143 68 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Ɗan mama yayi murmushi, ya ƙara taku biyu gabanta, ya kalleta ya ce "You better count yourself out of this. Ba ni da niyyar cutar da Viper, da cutar da shi zan yi, da tuni na yi so bakinki ƙanin ƙafarki" daga haka ya miƙe ya nufi in da suka baro su walid. Aka fito da Viper a kan gado, aka ce za a ba su ɗaki, za a turawa likita result ɗin. Kamar yadda Nabila ta yi tsammani, an biya bills ɗin, ta din ga yi wa ɗan mama kallon tuhuma, shi kuwa da sun haɗa ido, sai yayi mata murmushi, hakan ya ƙara jefata cikin tunani. Likita ya shigo da file a hannunsa, suka sake gaisawa, ya tattaɓa cikin Viper, sai dai duk da an yi masa allurai ya samu bacci, da ya taɓa cikinsa ɓangaren dama, sai da ya zabura ya motsa. Ya duba scanic ɗin hannunsa, ya ce "Hantarsa ce ta kumbura gaskiya, amma ƙodojinsa da sauran abubuwa lafiya ƙalau, amma duk da haka zaku yi x-ray na cikin, mu sake tabattarwa ko da wani abun" A tsorace Nabila ta ce "Likita hantarsa ta kumbura kuma?" "Eh, amma karki damu babu wani abu in sha Allah, idan aka yi x-ray ɗin, akwai likitanmu da zai zo ya duba shi, ba wani abun tayar hankali bane ba, zai samu sauƙi in sha Allah" Walid ya ce "Allah ya sa" Ɗan mama ya ƙurawa wayarsa ido, sannan ya kalli Nabila, yayi mata alama da su haɗu a waje. Ya tashi ya fara fita sannan ta bi bayansa. Ya ce "Ana bibiyarki, yanzu aka turo mini saƙo, zaki bani mukullin motarki, zan kawo miki ita gida a matsayin bakanike" "Nifa ban fahimci duk wannan abun ba" "Tsayawa dogon bayani, ba zai haifar da ɗa mai ido ba, ki ga gaggauta muje na raka ki, na ɓulla da ke wata hanyar ki hau napep ki tafi gida, zan kawo miki motar gida". "Kamar wani abun kake shiryawa a kaina" ya miƙa mata wayarsa, ta karɓa ta duba, message aka turo masa aka yi masa bayanin kar ta tafi a motarta, akwai yiwuwar a kamata, ko kuma ayi mata wani abu. Bai bari ta yi wa su liti sallama ba, ya fitar da ita daga asibitin, ya tare mata abun hawa ta hau ta tafi tana mamaki. Ta koma gida, duk a gajiye, abubuwa duk sun dame ta, tana ta tunanin ciwon Viper, tayi ta addu'a Allah ya bashi lafiya, sai ta ji ba ta kyauta ba maganganun da ta gaya masa, haɗuwarsu ta ƙarshe. "Allah ka bashi lafiya, ka bani ikon cika masa alƙawarin da nayi masa" "Arfa" "Na'am" ta amsa tana daga zaune. "Ina motarki?" Nasir yayi maganar yana shigowa cikin ɗakinta. "Lalacewa ta yi, na bawa bakanike" "Wane bakaniken?" "Bakanike dai mai gyara mota" "An ce an ganki da wasu maza a motar, a can ring road, sai dai ba a san in da ku ka yi ba, na saka jami'ai a arear in da ake tunanin kin bi, aka kama wani da motar yanzu haka yana tsare a wurina" Ta miƙe tsaye ta ce "Wai dan Allah yaya me kake nufi da ni ne? Motata ta lalace zan yi gammo na ɗauketa a kaina ne, na kira masu gyara su tafi da ita sai ya zama laifi, na menene zaka saka a din ga bibiyata ma?" "Saboda baki da gaskiya arfa, gaba ɗaya kin canza, kuma ba kya tsoron salwantar da rayuwarki" "Kalli, kamar da gaske ka damu da rayuwar tawa, ba ta rayuwata kake yi ba, mafitar ka kawai kake nema Yaya Nasir, amma ai ramin ƙarya ƙurarre ne ka cigaba da bibiyata. Na roƙe ka ka saki bawan Allah, gyaran mota kawai na bashi, abun arziki bai kamata ya zama na tsiya ba" ta fita daga ɗakin gaba ɗaya ta bar shi. Da daddare ta kira walid, ta ji ya jikinsa, ya tabattar mata jiki da sauƙi sosai, ya farka ma. Nabila ta ce "Oga walid, shaye-shayen nan ne fa ya fara taɓa shi, ya janyo masa wannan matsalar" "Ai bama sai kin faɗa ba, shi ne ba wani abun ba" "Dan Allah oga walid ku daina wannan rayuwar, idan ba haka ba da ƙuruciyarku haka zaku rasa lafiyarku ku mutu, dan Allah" yayi murmushi ya ce"Karki damu, za a daina in sha Allah" "Allah ya sa, ayi masa sannu dan Allah" Ya ce "Zai ji in sha Allah" bayan ya kashe wayar, ya fita yana mitar ina ɗan mama ya tafi har wannan lokacin bai dawo ba. A harabar Asibitin ya haɗu da ɗan mama, kamar ya kwaɗe shi, dan haushin abun da yayi, shi kuma bai gaya masa ainihin abun da ya faru ba, ya ce masa wani wuri yaje. "Ka wuce ka je ka zauna da shi, liti ya je nemo wani magani, ni kuma zan je gida". "Kar ka je gidan nan oga Walid, hanya babu kyau, cinnakun nan sun ɗana mana, akwai wani abu a ƙasa ka ɓad da sahu, ka lafe a wani wurin, akwaisu sosai a hanyar gidan nan" Walid ya ce "Na fahimta, muddin kaga wani abu da baka yarda da shi ba, ka kira sanar mini" ya jinjina masa kai. Nasir yana zaune ya gama cin abincin dare, aka kira shi a waya. Ya ɗaga a take, ganin daga office ɗin su ne. "Yallaɓai yaron nan fa, wasu sun zo sun yi belinsa" "Wane yaron?" "Wanda muka kama,  kuma sun ɗauki motar ma" Tashi tsaye yayi ya ce "What? Meyasa ku ka bari suka ɗauka? Waye ma ya ce a sake shi?" "Manyanmu ne yallaɓai" mukullin motarsa ya ɗaukko ya fito da sauri, kawai ya tarar da motar arfa a gareji. Bin motar ya din ga yi da kallo, dan ya tabattar ita ce, ko ba ita ce ba. Bai haƙura ba sai da ya dangana da zuwa ya dudduba ya tabattar dai ita ɗin ce. Bai tsaya ba, ya shiga cikin gidan, ya tarar da ita a falo, suna kallo a falon ita da mutanen gidan. "Arfa waye ya kawo miki motarki?" "Ina ga bakanike ne, yaro ne ya kawo mini key ya ce an kawo motar" tayi maganar cikin ko in kula. Ganin da mutane a wurin, ya sanya bai ja maganar ta yi tsawo ba, ya bar falon. *** Liti yana zaune yana game a wayarsa, likita ya shigo, ya kalli likitan, likitan ya ce "Sannu ko, ya mai jikin?" "Da sauƙi" "Masha Allah, naga ya samu bacci ma, shi ne mai hepatitis ko? Yayi maganar yana duba file ɗin Al'amin. Kodayeke ma bacci yake yi, bari ba sai an tashe shi ba, idan aka yi x-ray ɗin na duba shi, idan ya farka gaba ɗaya" yayi maganar yana taɓa cikin Al'amin. Sai dai yayi shiru yana kallon Viper, yana ƙoƙarin ganin fuskarsa sosai, dan kamar ya san shi, sai dai yanayin kwanciyar da ya yi, bai bashi damar yin hakan ba. Ya kalli file ɗin Al'amin, an rubuta Muhammad Ibrahim. Ya juya zai fita, ya tsaya ya sake waiwayowa ya kalli Al'amin ya ɗan yi shiru sannan ya fita. Yayi iya ƙoƙarin sa wurin tuna a ina ya san shi, amma ya kasa dan haka dolensa ya haƙura. *** "Rahama" "Na'am" "Zan fita da ke, zamu je asibiti, wallahi idan ki ka yi misbehaving, ke da ganin mahaifiyarki har abada" "Idan da zan yi misbehaving, da tuntuni da kake fita da ni da nayi, amma na fara gajiya da ƙaryar da kake yi mini, na cewa gwargwadon bin umarninka da nake yi, shi zai sanya ka sada ni da mahaifiyata. Ina tsoron tonuwar asirina na wulaƙanta a idon duniya, shiyasa bana yi maka ihu, da neman agaji, sonake ka mayar da ni cikin sirri da rufin asiri, yadda ba zan tozarta da yawa ba, amma haryanzu na kasa gane in da ka dosa" Ya ce "Zaki fahimta ne, muddin ki ka yi yekuwa, to ke zaki kunyata fiye da ni, kuma ni zan iya wanke kaina, ke kuwa zaki tozarta, dan sai kin samu masu ɗoraki a social media kowa ya ganki, kin san duk abun da namiji yayi ado ne" Ta girgiza kai ta ce "Wannan wani banzan tunani ne, na waɗanda ba su san girman Allah ba, babu al'ada a batun saɓon Allah. Allah bai ware wutar mace ba, kuma bai ware ta namiji ba, bai ce zai sassautawa wani ba dan yana wani jinsi idan ya saɓa masa ba, dan haka babu ado da zunubi, idan al'ada ta nuna maka duk abun da ka yi ado ne, addini kuma ya koyar da kai tsoron Allah da tsoron azabarsa" Wato ramma akwai baki, wasu lokutan duk abun da yake ji da shi, sai ta ƙure shi ta hanyar kafa mishi, hujjoji da addini, dan haka ya ja bakinsa yayi shiru, suka cigaba da shiri. Tana sanye da niƙab, a kan dogon hijjabinta, yake nuna mata wurare a cikin asibitin, wai nan ma branch ne na Asibitin, ba shi ne main branch ɗin ba, sai dai yayi kyau ya tsaru sosai da sosai. Washegari da safe Nabila ta je court ɗin da take da trial, tayi ta kammala, ta samu wurin parking, ta bayar da ajiyar motar, ta hau napep ta fita asibiti. "Ki zauna a nan, zan je na fara zagaywa na duba marasa lafiya na, sai na zo na tafi da ke, in da zan duba ki" Ta kalleshi ta ce "To ka tafi da ni mana, ni ba wani abun zan yi ba" "So ki ke sai wani ya ganki wai?" "Matsalar rashin gaskiya kenan" "Eh na ji, ga kayan tea nan, fridge akwai lemuka, ga kayan kallo nan, ki yi duk abun da ki ke so, ban da fitina, zan rufe ki a nan, zan je na ga marasa lafiya, sai na yi ward round na dawo" Ta ce "Saura ka daɗe" Abdul ya ce "No ba zan daɗe ba in sha Allah" yayi kissing goshinta ya ce "I love you, ki yi mini addu'a na yi komai cikin nasara" "To jeka, kar su gaji da jiranka" haka kurum ya din ga jin is no safe, ya bar ta nan, kamar wani abu zai faru, ya din ga waiwayawa yana kallonta, har ya fita ya rufeta a wurin. Nabila ta shiga cikin Asibitin, tana saanye da hijjabin da ta ɗora a kan uniform ɗin ta da facemask, sai waya take yi, tun da ta taho, wata matashiya da ita ma tahowa take yi, suna facing ɗin juna, take bin ta da kallo. Ji take yi, tamkar ta je ta ɗage facemask ɗin fuskar Nabila taga wacece, har ta wuce hanyar da yakamata ta tabi. Wayarta ce ta fara vibrating, ta ɗaga ta ce "Hello yaya" "Dalla malama kina ina, gashi ya zo, zai fara ganin marasa lafiya, ki zo ya fara da ke na mayar da ke gida, amma kin tafi yawonki" kasa bashi amsa tayi, ta ɗaga kai tana dube-dube, ta nemi Nabila ta rasa. Jiki a sanyaye ta shigo office ɗin, saifu kamar ya mareta ya ce "Wai ina ki ka tafi, yazo ya zauna yana jiranki?" Bata amsa ba, ta zauna jiki a sanyaye. Abdul ya ce "Dan Allah ka daina yi mata tsawa, ka san mara lafiya ce, ba na son naga ana kyarar mini patient, Hafsat ya aka yi ne?" "Doctor Abdul, jauhar fa na gani ta saka niƙab ta wuce" Ya ce "Wacece haka?" Saif ya ce "Na fuskanci ba ta warke daga depression ɗin nan ba, likita ya sallameta, ƙanwarmu da ta mutu fa take magana a kai" "Wallahi yaya, ka taso mu bi hanyar da ta bi, ka ganta kaima, ta saka niƙab" "Kuma da niƙab ɗin ki ka ga jauhar ce?" Ta ce "A'a, gani nayi kamar na santa, kuma wallahi irin idonsu ɗaya, ai naga idonta" Abdul ya yi murmushi, ya fara bin hanyoyin su na likitoci, wurin daidaita tunanin hafsa, da saka mata nutsuwa. Nabila tayi sallama. Al'amin yana zaune, ya jingina da jikin gadon, yana ɗan yamutsa fuska. Suka gaisa da ɗan mama, shikaɗai ne a wurin, ta ƙarasa gabansa ta ce "Sannu ya jiki?" Ya jinjina mata kai alamar da sauƙi. "Kaga ɗaya daga cikin illar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi ko? Kodayeke zuwa yanzu ai ba illa ɗaya ka gani ba, illoli daga dabar shaye-shaye da bangar siyasa wanne yayi maka rana a cikinsu? Daba da bangar siyasar a dalilin su, ka rasa makusantanka, ka rasa soyayyar mahaifi da ta ƴan uwa, illar da aka yi maka, ka kasa karɓar ƙaddararka, ta'amalli da miyagun ƙwayoyi ya sanya, ka nemi ka rasa imaninka, ka halaka kanka, yanzu gashi lafiyar ka ta taɓu, gaba ɗaya abubuwan nan babu wanda zaka ɗaga na ce ga ribar da ka samu a dalilin su, dan Allah ka cikawa yar madara burinta, duk da bata duniya, ka zama mutumin kirki, ka zame mata sadaƙatul jariya, ya zamana bata raye, amma tana da kamashon ayyukan alkhairin da zaka yi idan ka zama mutumin kirki, tun da ita ta ɗaukko hanyar saita rayuwarka bisa hanya mai kyau" kamar ba zai yi magana ba, sai ya buɗe idonsa ya zuba mata ido. Ita ma shi take kallo, amma ta yi ƙoƙarin janye nata idanun daga nasa. Ya zuba mata ido kamar zai haɗiyeta, hatta maganarta wani abun idan tayi, kamar Jauhar. "It all depends on you" ya furta yana cigaba da kallonta. Ta ɗago ta kalleshi, "Ke zaki ƙarasa abun da ta yi niyyar yi, ta hanyar cika mini alƙawarin da ki ka yi mini. Na gode da ki ka taimaka mini, ban rasa imanina gaba ɗaya ba, tabbas a duniya daba da shaye-shaye basu tsinana mini komai ba, sai asara kashi-kashi wata na bin wata. Abu ɗaya nake fata, ko da ba zan rayu ba, naga an hukunta wanda suka kashe mini mata ba tare da hakkinta ba, shi ne babban fatana, ke ki ka cusa mini  aƙidar in ɗauki mataki ta hanyar shari'a ba hanyar da nake so nake ganin ita ce dai-dai ba. Ba wai ina roƙonki bane ba, kina da zaɓin yin abun da ki ke ganin shi ne dai-dai a gareki" A ƙasan zuciyarta ta ce 'Ai ba zaka canza ba" Kiran sumayya ta gani a waya, ta ajiye ledar kayan marmari da ta shigo da su, ta fita amsa waya. Ba ta san dalilin kiran sumayyan ba, dan haka ta nemi hanyar da zata nesanta ta, da wurin shige da ficen mutane. Tabi wata hany, ta ɓulla wani wuri da babu kowa, ta tsaya a wurin ta ciro wayarta ta ɗaga ta ce "Hello, Sumayya T ladan baki abun magana, maƙogwaron kakaki radio". Gaban ramma ya faɗi, jin muryar mace a wurin office ɗin, sunan wadda aka ambata ne ya daki zuciyarta, Sumayya T ladan, tana jin program ɗin ta, sai dai a rufe take a cikin office ɗin babu hanyar fita. "Ba shakka Nabila Yusuf maitama, ni kike kira da ni da sunan ubana ko?" "To ai kin rama, ya ne ya ake ciki, ya gidan radio?. Abdul ya shiga ɗakin da Viper yake, da shi da wata Nurse da take on duty. Ya kalli ɗan mama ya ce "Ina mara lafiyan?" Ɗan mama ya ce "yana banɗaki" Ya ce "Ok, sister je ki room 4 ki duba mini temperature yaron nan, kafin na zo" ta ce "Ok sir" Ya tsaya yana dudduba medication ɗin da aka yi chatting, ya juya baya yana amsa waya Viper ya fito, ya nemi wuri ya zauna a kan gadonsa, ya gama amsa wayar ya juyo, idonsa suka shiga cikin na Viper. Ƙiris ne ya rage bai yar da wayar hannunsa ba, an kusa shekara bakwai rabonsa da Viper, tun wata haɗuwa da suka yi, ya zo hutu suka kusa faɗa P.A ya gargaɗe shi a kan hakan, Viper ya ƙara girma, kwarjini ya ƙara baibaiye shi. Shi bai san abun da ya faru ba, shi dai ya daina ganinsa a wurin mahaifinsa, ya ji labarin kisan kai yayi, aka rufe shi, sai kuma yaji mahaifinsa yana nemansa, kasancewar shi ba mai shiga abun da babu ruwansa bane ba, sam bai damu da sai lallai ya ji meyake faruwa ba. Da ido Viper ya yi wa Ɗan mama magana, ɗan mama ya taso, ya zo, Abdul bai gama tunanin ba, Viper ya zare wuƙar da ke ƙugun ɗan mama, ya fuzgo labcourt ɗin Abdul, ya zauna a gabansa. Ya kalli ɗan mama ya ce "Ka gindaya katanga, ba shiga babu fita" ɗan mama ya jinjina kai ya fice, ya rufe su ta waje. "Ka yi mamakin ganina ko? Nima mamakin ganinka nake yi, haka mahaifinka ya adana rayuwarka, ni kuma ya tagayyara tawa, ya bar ni da yawon ramuka ina ɓoye kaina, tamkar maciji, kodayek macijin ne ni, ina nan zan yi fitar burtu daga ramin, zan yi masa sara mafi muni, da zai yi ajalinsa" "Da mahaifina kake yi, ni meye nawa a cikin abun da ya haɗaku?" Viper ya saka masa kaifin wuƙarsa a jijiyar wuyansa ya ce "Kai likita ne, na san ka san ma'anar wannan jijiyar, kuma ka san mai hudata yake nufi ga rayuwar ɗan adam, idan ka yi wani yinƙuri da bai gamshe ni ba, zan yi wa jininka magudana zuwa doron duniya. Ya saka hannu ya ciro wayar Abdul daga gaban labcourt ɗin sa, ya ce masa "Buɗe ta" Ya karɓa ya buɗe masa, Viper ya karɓa yayi danne-danne a ciki, sannan ya miƙa masa ya ce "Gashi nan, zan tura masa saƙo mai muhimmanci ta hanyarka, kafin nan ka gaya masa, zan cigaba da farautarsa babu dare babu rana, sai na ɗaiɗaita farincikin sa, ni ƙarfen cikin wuta ne, hannun da yake ƙoƙarin sakawa dan ya kamani, idan nayi masa illa, sai ya nakasa, nakasa kuma ta har abada. Ƙarfen da yayi yinƙurin yin amfani ya ɗaukko ni, wutar tayi masa zafin da na riga na narka shi, ba kowane irin ƙarfe ne zai ciro ni ba. yana gama maganar ya hankaɗa Abdul da hannu ɗaya, sai da ya faɗi ƙasa. Nabila kuwa babu yadda ba ta yi ba, ta shiga, ɗan mama ya hanata, ya ce likita ne yake duba shi, ya ce su fito waje. Ita kuma ga sumayya na jiranta, tana ta tuna mata lokacin program ɗin su ya kuss, ga barrister Habib yana ta kiranta shi ma, dan haka kawai tayi masa sallama, ta ce za suyi waya. Ɗan mama ya ce "Jiya bayan fita ta da motarki yayanki da kansa ya kama ni fa" "Ina ta son na yi maka magana, ya aka yi kuma ya sake ka". "Waɗanda nake yi wa aiki ne suka karɓo ni, na kawo miki motar ki gida, na bayar da mukullin aka kai miki ciki" Nabila ta ce "Suwa ka ke yi wa aikin kenan?" "Ai sauri ki ke yi, kuma ya saɓa dokar aikin da nake yi, ki kula sosai yayanki tarko yake yi miki ko ta ina, siled mistake zai iya kama ki" ta ɗan yi shiru sannan ta jinjina masa kai ta ce "Na gode" Cikin ɗakin kuwa da sauri Abdul ya tashi, ya shafo wuyansa da wuƙar Viper ta fara yankarsa, ya ga jini, ya ja da baya a hankali yana kallon Viper, ya nufi hanyar fita ya jijjiga ƙofar da ƙarfi, ɗan mama ya buɗe, ya fice cikin matsanancin hanzari, ɗan mama kuma ya shiga. Wuyansa ya cigaba da tsatstsafar da jini, ya fita gate wurin security, ya ce su hanzarta, su shiga amenity 2, su kama wanda yake cikin ɗakin, babban ɗan ta'adda ne, da jami'an tsaro suke nema" nan da nan suka tashi da gudu, suka yi cikin Asibitin. Ma'aikatan suka ce, ya tsaya ayi masa treatment ɗin wuyansa, ya ce musu a'a, ya je ya buɗe Office ɗin sa, ramma na ciki ta kwanta a kan couch ɗin ɗakin tana bacci, ya danƙota daga kan kujerar, sai da ta razana, ya fita da ita da sauri, ta ce "Abdul lafiya kuwa? Menene wai?" "Akwai matsala ne" ya faɗa lokacin da ya sakata a mota ya rufe. Suna tafe a hanya ta ce "Meyasame ka a wuya ne? Wai me yake faruwa?" "Wani patient ne mahaukaci, ya yanke ni a wuya" Cikin tausayawa ta ce "Subhanallah, sannu Allah ya sauwwaƙe, kuma baka tsaya ka saka magani ba" "Bakomai, idan muka je gida na saka" Security kuwa suna zuwa suka tarar da ƙofar ɗakin a buɗe hanhai, sai dai babu kowa a ciki. Suka dudduba har cikin banɗaki, amma babu kowa. Suka je suka rufe gate, aka hana kowa shiga da fita, tuni aka sanar da jami'an tsaro, Viper kuwa da ɗan mama tuni suka dire katanga, ya kira su walid ya ce kar su dawo, asibiti babu lafiya, Viper ya haɗu da ɗan gidan indabo. Liti ya ce "Maganar banza kenan, kuna daidai ina mu zo mu same ku?" Viper ya ce "Ba sai kun zo ba, zamu zo mu same ku" Sai da ya kai ramma gida, ya zauna ya yi wa kansa dressing, aka kira shi a waya, aka ce ya je yan sanda za su ɗauki report ɗin abun da ya faru. "Kai ba zan sake dawowa wurin nan a yau ba, sai an tabbatar da security wurin" Ɗan sanda ɗaya ya karɓi wayar, ya ce "Doctor, to ko zaka gaya mana wani ɗan ta'addan ne?" "Aminu Viper ne, wands ake cewa mai zamani da". "Mai zamani kuma, yallaɓai Viper fa" "Eh shi fa" Ɗan sandan ya ce "Ok to" Nan da nan suka kira DSP Nasir a waya suka sanar masa. Nabila bata san abun da yake faruwa ba, ta ƙarasa gidan radion su sumayya, sai da suka yi faɗa da sumayya, saboda lokacin shirin ya ɗan ja sosai, sai itakaɗai ta fara program ɗin. Sai da ta nutsu, suka gama faɗan dai-dai lokacin aka dawo daga talla, sumayya ta gabatar da ita suka ɗora da program. Yau ma dai program ɗin na su, a kan abun da ya shafi harkar shari'a ne, kanta tsaye take bayyana ƙulle-ƙulle da rashawar da ta yi katutu a harkar shari'a. Nan ta tabattar da cewa zasu yi appeal, a kan shari'ar ramma, kuma tana fatan hukumar shari'a zata sanya ido sosai a kan yadda shari'ar zata gudana. Sumayya ta ce "Yanzu dai kina da hope kenan, a kan appeal ɗin da zaku yi?" "Sosai kuwa sumayya, kuma ina nan a kan bakana, lauyoyin gwamnati da bunkure foundation su gabatar da victim a gaban kotu, kuma ina da kyakykyawan fata a kan wannan shari'ar, sannan bayan haka akwai tarin ƙulle-ƙulle da zan warware a wannan zaure, masu tarin ban mamaki" "To shikenan, da ni da masu sauraro muna dako, duba da yanayin lokaci, baki samu shigowa da wuri ba, da haka da haka nake cewa muna nan muna saurarenki, domin jin wane irin ƙulli zaki warware mana. The lady of her words, the young capacitated barrister, gugan ƙarfe sha kwaramniya iron lady, kuma boss lady, voice of voiceless Barrister Nabila Yusuf maitama ayi sallama da masu sauraro" Dariya Nabila ta din ga yi ta ce "Kirarin nan naki dariya yake bani Sumyya, ai ke ce voice of voiceless, baki abun magana, a sayar da a tsage gaskiya, the lady of the century Sumayya T ladan, Allah ya ƙara kiyaye mana ke, masu sauraro Assalamu alaikum" suka ƙarƙare shirin cikin nishaɗi da dariya. Tuni Nasir ya isa asibitin, ya fara investigation, aka ɗaukko masa file ɗin Viper da aka buɗe, sai dai babu lambar waya a jiki, ya ce meysa babu lambar wayar mai file, record suka ce, emergency aka buɗe file ɗin, kuma ba su ne a shift ɗin da aka buɗe file ɗin ba. Ya saka security su kawo masa littafin da masu shiga da fice suke rubuta sunan su a ciki, aka kawo masa yana dubawa, babu wani sanannen suna a ciki, sai dai ya tsaya cak, ganin sunan Nabila a cikin book ɗin. Nabila kuwa ta ɗauki hanyar titi, bayan ta ɗauki motarta, tana tafe yau jinta take sakayau, kwanakin da ta yi cikin takaici, zuciyarta tamkar an wanke mata ita. Ta kalli glass ɗin motarta, ta ga wata babbar mota ta taso ta a gaba, idan ta kauce, ta bar hannun ta bawa motar dama ta wuce, sai motar ta rage gudu, ganin ba zasu bata damar tafiya cikin kwanciyar hankali ba, ya sanya ta ɗauki titi sosai, ta wuce su, amma suka cigaba da binta by fire by force ita suke hari!. (Am sorry for delayed posting, am sick ayi mini addu'a please) Ayshercool 08081012143 69 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Al'amin da ɗan mama suna kwance a cikin ciyayi, in da suka ɓuya nesa da Asibitin sosai. Suna ta jin kai komon motocin yan sanda, ɗan mama ya kalli Viper, ya ga yadda yake rintse idanunsa, yana damƙar ciyayin wurin, ya ce "Sannu oga Viper, cikin ne? Ko wani asibitin zamu tafi?" Ya girgiza masa kai alamar a'a. "To tun da da cannula a hannunka, kaga magungunanka da na kwaso, naga suna yi maka wannan allurar, ina ga ita ce ta ciwon cikin, bari na yi maka" Viper bai ce masa komai ba, ɗan mama ya haɗa allura ya hau zuba masa a cikin cannula, a hankali viper ya fara buɗe idanunsa, amma kansa ya fara juyawa, ya kasa magana. Ɗan mama ya koma gefe, ya kunna sigari yana sha, mintuna goma Viper ya tafi gaba ɗaya, ya ciro wayarsa ya danna, sannan ya saka a kunnensa ya ce "Hello sir, eh su yi sauri ya samu bacci, amma yana cikin ciwo sosai" Ya ajiye wayar ya cigaba da shan sigarinsa, mintuna arba'in sai ga wata helux baƙa ta iso wurin, wasu narka narkan ƙarti suka fito, suka saɓa Viper suka saka shi a cikin motar, ɗan mama ya kama ya hau suka tafi. Suna tafe a hanya su liti suna kiran ɗan mama a waya, ya gaya musu yana ina, da shi da Viper, ya din ga raina musu hankali yana yi musu kwana-kwana, suka din ga zaginsu amma ya ce "Oga walid ka yi haƙuri, wayar zata mutu babu caji" ya katse wayarz ya cire batirinta gaba ɗaya. Wani Asibiti suka kai shi, likitoci suka rufu a kansa, suka dudduba shi, suka ce babu wata matsala zai warke, ba wata gagarumar matsala bace ba, sai dai dole ya nisanci shaye-shaye idan yana son zama lafiya. Nasir jiki na rawa ya ɗaukko wayarsa, yana kiran Nabila, sai dai yayi mata missed calls, sun fi biyar, ko ɗaya bata ɗaga ba, hakan ya ƙara fusata shi ainun, ficewa yayi ya ɗauki mota ya bar Asibitin, yana ƙoƙarin gazgata zargin da yake yi wa Nabilan. Yana ƙoƙarin sake kiran wayarta, sai ga kiranta, ya ɗaga zai yi magana ya ji muryar da bata Nabila ba, ta wani daban. "Malam ina mai wayar?" "Ta haɗu da hatsari, tana emergency na asibitin cikin gari" wani wawan burki ya ci a tsakiyar titi, wanda sai da ya kusa haddasa hatsarin shi ma. "Ta mutu ne?" "A'a, ana kula da ita, ni ɗan sanda ne, mu muka kaita asibitin" "Nima ɗan sandan ne, ka gaya mini ta mutu ko?" "A'a, muna dai jiran abun da likitoci zasu ce ne" ana tayi masa horn, amma hankalinsa baya kai, ya fizgi motar ya canza hanya. *** Ramma kuwa bayan Abdul ya gama wayar ta ce "Ka ce mini mahaukaci ne ya yanke ka, kuma yanzu na ji yan sanda ne suka kiraka ana zancen ɗan ta'adda" "Eh shi ne mahaukacin ai" Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Kamar na san sunan da ka faɗa fa" "Wanne?" "Mai zamani, amma kuma kamar ba haka ake ce masa ba, mama ta san shi" Basar da zancen yayi ta hanyar cewa "Wayyo wuyana" Cikin kulawa ta  ce "Sannu, ka kwanta to" "To ki zauna sai na kwanta a kan cinyarki" "Gaskiya ba zaka takura mini ba, wai kai jinyarka sai ka ce wani jariri, ka yi ta ragwanci, ɗan wannan ciwon sai wash kake, wannan idan kaga fuska kuka zaka yi kenan?" "Haba baby, ki tausaya mini mana, da na mutu fa" Ramma ta ce "Haka nake fata dama" "Ƙarya ki ke yi " yayi maganar yana janyota, yana ƙoƙarin kwanciya a jikinta, ta ture shi ta ce "Baka isa ba, idan ka gama sangartar ka watstsake, mutum ba juriya" Shagwaɓe fuska yayi, yana kuma kwanciya a jikinta ya ce "Zafi" "To sannu" "Yauwwa baby, i love You, ki kula da ni sosai" "To samo zani sai na goyaka ƙarewar kula, ka rabu da ni dan Allah" ƙarshe ta gama mitar ta rabu da shi. *** Nabila kuwa a emergency, aka gano gocewar ƙashi a hannunta, sai buguwa da tayi a ka, ta fasa goshi, ga jini na fita daga hancinta, in da Allah ya taƙaita abun, da seatbelt a jikinta take driving, dan Abba na yawan gargaɗinta a kan hakan. Godiya Nasir ya din ga yi wa Allah, da ya tarar bata mutu ba, daga nan asibitin, ya ɗauketa ya canza mata wani. Da ƙyar ya iya kiran Abba ya gaya masa, saboda yadda baya ɗaukar lamuranta da sauƙi. *** Lokacin da aka kai Viper da ɗan mama gida,  su liti basa nan, sun bazama nemansu, duk da a hanya, sai da jami'an tsaro suka tare motar, da son bincikar motar, amma ganin masu motar, ya sanya aka basu dama suka wuce. Suka kwantar da Viper suka tafi, ɗan mama ya gyara gidan, ya nemi wuri yayi zamansa hankali a kwance. Dare yayi sosai, su liti suka dawo, suka tarar da ɗan mama da Viper yana bacci. Zabura liti yayi, zai kwaɗe shi, Walid ya hana shi, ya ce "Ɗan mama, wane irin wulaƙanci ne ka yi mana haka?" "Oga Walid, wayata ce ta mutu fa, ɗan gidan indabo ne likitan da ya shiga duba shi, tona mana asiri ya so yayi, a kama mu, muka yi layar zana, muka dirge, muka samu wuri muka ɓuya, ciwon cikin ya sake tayar masa, na yi masa wata allura da na ga suna yi masa a cikin kayan magungunan sa, kawai naga ya ware, shi ne na samu abun hawa, na kai shi wani asibitin, da kyar na kawo shi gidan nan, hannunsa na saƙalo a kafaɗata muna tafe muna faɗuwa har gida". Liti ya ce "Ɗan azzaluma, duk sai da ka azabtar da shi, ga ciwo yana fama, shegen taurin kai kamar jinjirin jaki, ka gaya mana kuna ina, ka ƙi da yake ɗan kut....ne kai, ɗan wahala kawai". Walid ya ce "Dan Allah liti kayi haƙuri, tun da Allah ya dawo da su gida lafiya" "Ai yaron ne, wasu lokutan yadda ka san rainon garke, gaba ɗaya rayuwar sa, babu lissafi" Ɗan mama ya ce "Ayi haƙuri" "Kai ni fa ban ma yarda kai kaɗai, ka iya kawo Viper gida ba, Allah ya sa ba wani haukan kayi, ka kawo mana wani ya ga in da muke ba" "A'a oga liti, nikaɗai na kawo shi gidan nan" "Ware maƙaryaci kawai" *** "Abdul" "Na'am daddy" "Saura wata guda bikinka, babu wani alamar shirye-shirye da kake yi, kawai dai gaka nan, ta ƙarfi da yaji ka ke son salwantar mana da wannan damar" "No daddy ba haka bane ba, ina shiri, amma yau ka ji news kuwa?" "A'a wasu lokutan news ɗin nan, hawan jini yake saka mini, amma meyake faruwa?" "Na haɗu da Viper fa" miƙewa tsaye Indabo ya yi ya ce "Wane Vipern?" Abdul ya ce "Ya naga ka tashi tsaye? Viper dai naka, ya je ƙaramin branch ɗina, an kwantar da shi har ya kwana" Indabo ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wai da me yaron nan yake taƙama har haka, yawo ma yake yi a cikin gari har da zuwa asibiti? Anya ba harinka yake yi yayi maka wani abun ba, ya sanya ya je?" Abdul ya girgiza kai ya ce "Bana tunanin hakan, unexpected muka haɗu, naje da daddare ban gane shi ba, yana bacci, sai yau da safe muka haɗu, amma dan Allah Daddy, meya haɗaka da Viper har haka, yake farautarka kai ma kake farautarsa?" Indabo yayi wuƙi-wuƙi da ido ya ce "Ya gaya maka wani abun ne?" "A'a, amma ya ce yana nan zai yi fitar burtu, yana nan tafe gareka, dan Allah mai ka yi masa ne?" Indabo ya ce "Babu komai, kawai dai ka san yan daba, ba alƙawari ne da su ba, babu wani abu da nayi masa" yanayin yadda yake maganar, ya sanya Abdul gane akwai wani abu a ƙasa, amma ya ɓoye masa, Abdul ya jinjina kai ya sake cewa "Daddy" "Na'am Abdul" "Bayan na auri 'yar gidan party chairman, idan na kawo wadda nake so, zaka aura mini ita?" "Wacece kuma a ina take?" "A'a kafin in gaya maka, zaka yarda na zauna da ita, kuma ba zaka yi mini faɗa ba?" Indabo ya ce "To ai haryanzu ba ka yi mini bayani ba" "Amm yarinyar da nayi raping tana raye" "What! Tana raye? Tana ina?" Cikin sanyin jiki Abdul ya ce "Dan Allah Daddy kayi haƙuri ɓoye makan da nayi, tsawon lokaci, dan Allah ka yi haƙuri" "Na ji, na ji, tana ina yanzu?" Abdul ya girgiza kai ya ce "To ai daddy baka ce komai ba, dan Allah ka yi haƙuri, na san nayi kuskure, sai da na ce zan kasheta, na ga ashe kisan kai ba abu ne mai sauƙi ba, dan Allah ka yi haƙuri " Indabo ya yi shiru sannan ya ce "Na ji, amma yanzu tana ina? An yi sara a kan gaɓa, hankalin mutane ya dawo kan appeal ɗin da waccan shegiyar yarinyar zata yi, dan haka dole zata bayyana a gaban kotu, amma da baka kasheta ba tana ina?" "Daddy, abun da kawai zan iya gaya maka kenan ban kasheta ba, saboda ina tsoron matsala ta taso daga baya, amma ba zan iya barin rahama taje gaban kotu ba" "Me kake nufi?" Cikin damuwa ya ce "Ban san me zai iya biyo bayan hakan ba, rahama tana tare da ni a wuri daban, tsawon wannan lokacin" wani lafiyayyen mari Indabo ya ɗauke Abdul da shi, ya dafe kuncinsa ya ja da baya. "Abdul yasar, yaushe ka yi girman da zaka yankewa kanka hukunci ba tare da sanina ba? Yanzu duk dambarwar da ake yi yarinyar nan na tare da kai? Audio da yake yawo aka ce muryar babarta ne, da gaske kenan zuwa ka yi ka ɗauke ta, saboda mahaukaci ne kai, sai ka je da kanka, ba ma turawa ka yi a ɗaukko maka ita ba, lallai ta tabbata baka da hankali dabba ne kai, wallahi ba zaka lalata mini siyasa ba duk wannan wahalar da nayi ta tashi a banza ba" "Daddy, dan Allah ka fahimce ni". "Shut up my friend, ubanka zan fahimta ka je ka kawo mini yarinyar duk in da ka kaita, kafin na casaka wallahi ba zan bari ka tona mini asiri ba, saboda hauka da wautarka ba, fice ka bani wuri kan na tattaka ka" Abdul ya tsuke fuska sai hura hanci yake yi, ya fice, sam bai ji cewa ko indabo zai jajjaga shi, zai kai masa Ramma ba, ko ya yarda ta tsaya a gaban kotu ba, sai dai ayi duk wadda za ayi. *** Bayan farfaɗowar Viper daga baccin da allura nan ta saka shi, ya din ga mamaki, wace irin allura ce haka, bai takura da kansa da dogon tunani ba, sai dai yadda ya din ga jin ina ma, ya yi wa Abdul mummunar illa, kan ya baro asibitin, sai kuma wata zuciyar ta tuna masa, ba shi ne yayi masa laifi ba. Wata zuciyar kuma ta ce kai ma ba matarka ce tayi musu laifi ba, suka kasheta. Ya tashi ciwon cikin da sauƙi, ya yi alwala ya rama sallolin sa, da daddare ya zauna yana jiran kiran wayar Nabila da daddare, dan ya san ba zata iya zuciya ba, sai ta kira shi ta ji ya jikinsa, amma shiru ba ta kira ba, har cikin dare idan ya juya, sai ya duba wayarsa ko ta kira bai sani ba, amma babu kiranta, shi ma kuma ya kasa kiranta. Abba kuwa godiya ya din ga yi wa Allah, da likitoci suka tabattar masa da ba wani abun tashin hankali ne ya samu Nabila ba, ta bugu ne a ka, kuma babu internal injury, sai hannunta da ta samu gocewar ƙashi shi kawai za a gyara. Mama ta hau masifa, ta ce "Ba dai ita yar gata ba, an ɗauki mota an bata ba, Allah kaɗai ya san tuƙin gangancin da take yi, ko dan ma tayi burga a titi, gashi ta tayar da mutane tsaye" Abba ya ce "bata tayar da kowa tsaye ba, babu wanda na yi wa dole ya zo ya zauna mini da ita, a da ma baku yi ba sai yanzu? Kuma tuƙin da take yi, ai masaniyar doka ce ita ma, ba wani tuƙi da take yi na ganganci, jarabta ce kawai Allah ya kawo, kuma ya taƙaita, Magajiya zata yi mini jinyarta, zuwa a sallameta, ban ce dole ayi mini ba" mama ta ja bakinta tayi shiru, jin abun da ya ce. Ya cigaba da kallon Nabila, cikin tsananin tausayawa, kwanan nan abubuwa sai samunta suke yi, daga wannan sai wannan. *** Nasir ne zaune a gaban Indabo, fuska babu walwala Indabo ya ce "Naga alamar aikin nan baka ɗauke shi da muhimmanci ba, idan har ba zaka iya ba, zan saka a canza mini kai, nayi abun da nake ganin shi ya dace". "Ina mai baka haƙuri, amma komai ya kusa zuwa ƙarshe" "Idan ma baka kawo shi ba, ni zan kawo". *** Hafsa ce zaune a gaban baba ta ce "Baba" Ya ce "Na'am ƴar baba" "Baba na san ai kai ba zaka ƙaryata ni ba ko?" "Eh mana yaya zan yi na ƙaryata ki ma?" Hafsa ta gyara zamanta ta ce "Ai dai ka san na warke yanzu, bana yawo, ba na shan komai, kuma na warke ai dai ko?" Ya ce "Alhamdilillah kam, duk na sani hafsat" "To yadda naga jauhar yau Allah ya nuna mini annabi haka, ta saka niƙab, da irin tafiyarta, da irin idonta, amma sai da na ganeta, na so na bi ta, yaya saifu ya kira ni, na nemeta na rasa" Baba ya ajiye cokalin sa, ya ce "Anya kuwa warkewar nan hafsa? Yaya za ayi ki ga wanda ya riga ya mutu, kuma ta cikin niƙab ɗin ki ka iya gane ita ce?" "Haba Baba, ka san dai yadda nake da jauhar, amma ko ina ga fatalwarta ce, amma dai da ko da ta zo mini a fatalwa, sai ta tsaya mu gaisa, bai kamata ta nuna kamar ba ta sanni ba, ina ga haryanzu haushina take ji, saboda na auri Alhaji mu'azzam yakamata ai ta yafe mini, ba ta ga irin wahalar da na sha ba, ai ko gaisawa sai ta tsaya mu yi. Ka ce na din ga yi mata addu'a, ina yi mata fa, amma duk ba ta ga wannan ba, ta share ni, ban san ya aka yi waliyiyyarka ta koyi wannan halin ba baba" tayi maganar tana kuka iya ƙarfin ta. Ya share hawayen da yake shirin gangaro masa, ya ce "Bata kyauta miki ba, zan yi mata faɗa, amma ina ga zamu koma Asibiti ganin likita". Hafsa ta ce "Baba da hankalina fa, ba hauka nake yi ba, ina sane da duk abun da nake yi fa" Mama ce ta shigo ɗakin ta ce "Ke mahaukaciya, tashi ki fita ki bashi wuri, ya gama cin abinci dan Allah, kin saka shi a gaba da sakarci" Hafsa ta ce "Ni ba mahaukaciya ba ce ba, cutar damuwa nayi ba hauka ba" Baba ya ce "Na sha gargaɗinki a kan kiranta da mahaukaciyar nan, wannan salon ki sake tunzurata ne ai" "A'a dama ai a tunzuren take" Hafsa ta tashi rai a ɓace, ta fita tsakar gida tana kiran Anty. "Hafsa wane irin kira ne wannan? Menene?" "Kin ga maman su surayya tana ce mini mahaukaciya ko? Ni fa ba mahaukaciya ba ce ba" A fusace Anty ta nufi ɗakin Baba ta ce "Wallahi kar ki sake kiran ya ta da mahaukaciya, idan ba haka ba duk abun da nayi miki ke ki ka saya" "Mecece idan ba mahaukaciya ba, ba dai auren cin amana ba, da son abun duniya ba, ta haɗu da babarta a makirci a matsayin kishiya ai, ga hauka ga ba auren, sai an yi magana ace depression ne, yarinya ta zama yar ƙwaya ta haukace" "Eh bakomai, tun da har ta yi auren ai, ta shiga ta fito, da babbar budurwa ai gara ƙaramar bazawara, da kike maganar zama yar ƙwaya, naki ɗan uban menene ba ya sha? Ko kina tunanin bamu san komai ba" Hafsa ta koma gefe tana kuka, saboda ta tsani taji an kirata da mahaukaciya, kuma haryanzu idan ta tuna jauhar, da cin amanar da aka yi mata sai ta ƙara shiga damuwa, tayi ta kuka, ta san hakkin jauhar ne ya sanya ta tsinci kanta a wannan mawuyacin halin da take ciki. Baba yana jin su, ya fito a zuciyarsa yana Addu'ar, Allah ya sa jauhar da mahaifiyarta suna tare a aljanna. Ya fice ya bar musu gidan. Walid yana ta lallaɓa Viper, ya ci abinci ya sha magani, gaba ɗaya jin sa yake yi wani iri babu daɗi, ya karɓi kofin shayi yana sha a hankali. Ɗan mama ya kunna radion wayarsa, liti ya hau mitar ya cika musu kunne, ya ce "Dan Allah oga liti kayi haƙuri, labarin wasanni zan ji" "Ai sai ka yi" Tashar su Sumayya ya kai, a dai-dai lokacin da murtala yake sanar da hatsarin da Nabila ta samu a jiya, bayan kammala program da suka yi ta tafi, suna barar a sakata a cikin addu'a. Buredin da viper ya haɗiya ne, ya tsaya masa a maƙogwaro, tamkar ya haɗiyi dutse. Liti ya fizge wayar hannun ɗan mama ya ce "Ban gane hatsari ba, ji ya ma fa taje Asibiti duba Viper, har yaushe ta yi hatsari kuma?" Walid ya ce "Babu kusa babu nesa ga Allah, amma dai dole mu san halin da take ciki" Liti ya ce "Taɓ yarinyar nan tana shan azaba, dudu yaushe ta kusa mutuwa a gobara, yanzu kuma hatsari?" Viper ya din ga murza kofin hannunsa, gumi yana tsatstsafo masa, amma bai tofa uffan ba. Ɗan mama ya tashi ya ce "Bari nayi maza nayi wanka, na je unguwar su na jiyo, wane asibitin take? Ko kuma na je asibitin da ta kwanta lokacin da tayi gobara, yadda ake ciki dai zan kira ku" "Saura kuma ka kira mu ka yi mana wannan gaɓancin naka, kayi mana wauta, ka tsaya ka nutsu, kuma saura ka ce baka da caji a waya" Ɗan mama yayi murmushi ya ce "Ni na isa, in sha Allah ba za ayi haka ba" Walid ya ce "Viper ka ƙarasa ci, in sha Allah babu wani abu, tun da ba su ce ta mutu ba, an ce dai ta ji raunuka ne kawai" shi dai bai ce komai ba, ya ajiye kofin shayin. *** Yanayin yadda Abdul ya shigo, sai da ramma ta ɗan tsorata, maye yake yi sosai. Ta tashi ta nufi in da yake, ta ce "Abdul giya ko? Baka ce mini ka daina shan giya ba?" Yayi shiru yana ta numfarfashi. "Kai dai ba zaka taɓa gyara rayuwarka ba, idan ka yi kamar zaka nutsu, sai ka ƙara fanɗarewa, kayi ta yi mini alƙawari baka cikawa". Ya kama hannunta ya rirriƙe, ya ɗaga jajayen idanunsa da ƙyar ya kalleta ya ce "Rahama" "Meye?" "Dan Allah karki rabu da ni, ban san me zai iya faruwa a gaba ba, ina sonki, ina sonki....Ai zaki yafe mini ko rahama" yayi maganar cikin maye yana kallonta. Ta kwantar da kansa a kan cinyarta, tana shafa sumarsa a hankali ta ce "Kana so na amma ka je ka sha giya, kafi bawa soyayya muhimmanci a kan tsoron Allah ko?" Ya girgiza kai alamar a'a. "Ga lokacin Sallah yayi, amma babu damar ka yi saboda kana maye, idan ka mutu a haka fa, zan yafe maka ne kawai, ranar da ka mayar da ni gaban mahaifiyata ka nemi afuwarta" "Idan nayi hakan, zaki yafe mini, mu cigaba da zama tare?" Tayi shiru ba ta ce komai ba. "Wallahi rahama, komai zai faru sai dai ya faru, idan aka yi ƙoƙarin raba ni da ke, zan ɗauke ki ne na yi gaba da ke, muje mu cigaba da rayuwarmu tare" Ta ce "Mhmm Abdul yasar rigima, kayi shiru ka daina wannan surutun ka samu ta sake ka, kayi salla ba na son ka mutu kana rashin ji, wasu lokutan dai kayi ta abu kamar mutumin kirki, amma zunubanka da kake tafakawa ne, sun wuce misali" "Rahama" "Abdul yasar" "Wallahi ba zan yadda a rabani da ke ba, ina sonki sosai" "To likita, amma na ce kayi shiru ai" Ya ce "To na yi" da haka ya din ga sauke numfashi, yana bacci. **** Ƙarfe biyu da rabi na dare, Viper yana cikin asibitin da Nabila take, sawu duk ya ɗauke, yan dubiya babu kowa, daga majinyata, sai marasa lafiya da ma'aikatan da za su kwana. Ya jinjina ƙofar ɗakin da Nabila take, ya tura a hankali, bai ji an yi magana ba, ya sake turawa ya ga duhu, an kashe fitilar ɗakin, ya shiga ya rufe ƙofar, ya kunna fitilar wayarsa ya haska, baba magajiya na ƙasa kan carfet tana bacci. Ya haske Nabila tana kan gado, ita ma baccin take yi, ana ƙara mata jini. Ya taka a hankali, ya je gaban gadonta ya durƙusa, an naɗe mata hannu ɗaya da bandeji wanda ta samu gocewar ƙashin. Hular kanta ta zame, tun daga farkon goshinta, a cike yake da gashi mai santsi, kasancewar ba gwanar yin kitso bace, gashin nata a tsefe yake. Ya kai hannunsa goshinta, in da aka rufe da plasta, da alama rauni ne a wurin, ya dawo ya riƙe hannunta ya ce "Get well soon, Allah ya baki lafiya" "Viper" ta furta a hankali kamar mai raɗa. "Angry bird" "Ya jikinka?" Ya ce "Na ji sauƙi" "Yanzu ma na san ba zaka kira ni a waya, ka yi mini sannu ba, ka tsane ni" Ya girgiza kai ya ce "Ban tsane ki ba Abla, ina so ki rayu ne, in cigaba da ganin fuskar jauhar a cikin taki" "Viper" "Mmm" "Zan cika maka alƙawarin ka in sha Allah, duk wuya duk rintsi, zan tsaya maka sai ka yi 'yanci, duk girman barazanar da zasu yi mini, zan tabattar da an yi maka adalci da kai da matarka" "Allah ya baki iko" Ta sake cewa "Viper" "Mmm Abla" "Dan Allah kar ka tafi daga mafarkina yanzu, na san idan na tashi, ba zan iya zuwa asibiti na dubaka ba" Yayi shiru bai kuma ce mata komai ba, ta ƙara riƙe hannunsa, da yafi nata girma sosai. Jikinta ne ya ƙara saki, ta cigaba da bacci, tana yi tana surutai, a hankali har ta yi shiru. Ya sake haskata da fitilar sa, irin innocent face ɗin jauhar ta bayyana a fuskar Nabila. A hankali ya zare hannunsa daga nata, ya yinƙura ya tashi ya fita daga ɗakin. Washegari da safe, sai tunanin mafarkin da tayi jiya take yi, tana tunanin gaske ne, ko kuma kawai mafarki ne?. Da safe ana ta zuwa dubata, wajen ƙarfe sha ɗaya Nasir ya zo, lokacin babu kowa kasancewar ranar aiki ce, sai baba magajiya. Suka gaisa, ya aiki baba magajiya ya rage saura daga shi sai Nabila a ɗakin. Ya zauna daf da ita a kan gadon, yana kallonta ya ce "Sannu ya jikin?" Ta amsa da "Jiki Alhamdilillah, da sauƙi, zuwa gobe in Allah ya kaimu nake so na tafi ma, i have a lot to do" Ya ce "Well, tambayarki zan yi, kuma bana buƙatar ki yi mini ƙarya, saboda zargina ya tabatta gaskiya ne a kanki" "Wane zargin?" "Nabila kin san in da Viper yake, kina haɗuwa da shi!" Ta kalleshi ta ƙura masa ido amma bata yi magana ba. "Ina magana kina kallona, na samu rahoton an ganshi a A.I hospital, naje bamu sameshi ba, amma naga signing ɗin ki, kin je asibitin me ki ka je yi?" "Ni ganin likita naje, ka daina zargina tun da baka da wata hujja, mai asibitin aka tura ni wurinsa follow up, saboda lokacin da aka sallame ni, bai zo ba" "Ƙarya ki ke yi Nabila" "Ni ba ƙarya nake yi ba, ka fara samo tabattaciyar hujja, kafin ka ƙaryata ni" Ya jinjina kai ya ce "Zamu gani ai, bayan duk wannan abubuwan hujja ki ke so na kawo miki? Shikenan zamu gani, amma ki sani aikinki ba zai baki kariya ba, muddin aka kama ki da laifi, sunanki yar ta'adda kema, mai ɓoye mai laifi" "Abun kunya ne ga hukumar yan sanda ace sun gagara kama mutum ɗaya, da yake iya yawonsa a cikin gari, sai ma a din ga bibiyar wanda bai ji ba, bai gani ba, ana yi masa baranaza" tsananin fusatar da yayi, ya sanya kawai ya tashi ya bar ta a ɗakin. Ta dafe ƙirjinta, saboda yadda yake tsananin bugawa, ta yanke a ranta dole tayi gaggawar fara shari'ar Viper, kafin ta kammala ta ramma. Ya fita babu jimawa, baba magajiya ta dawo, ta karɓi aron wayarta, ta shiga banɗaki, ta kira wayar Walid, Allah ya taimaketa ya ɗaga. Ya ce "Barrister ashe tsausayi ne ya faru haka, ya jiki?" "Jiki da sauƙi, meyake faruwa ne? Yayana ya ce mini ya samu labarin Viper ya je asibiti, ina yake ina fatan babu wata matsala?" "Eh, Yana nan cikin ƙoshin lafiya mun koma gida ma, haɗuwa yayi da ɗan Indabo a matsayin likitan da ya duba shi, shi ne ya sanarwa security" Ta ce "Haba dai? Likitan da ya duba shi kuma? Garin yaya dole mu ƙara taka tsantsan amma ba abun da ya faru?" Walid ya ce "Babu abun da ya faru, mun bar Asibitin ma, muna gida" "Dole na haɗu da shi, nan kusa Allah ya ƙara afuwa" ta katse wayar ƙirjinta na cigaba da bugawa. *** Indabo yana ta sanya ran ya ga ta ina Abdul zai ɓullo, ya kasa zaune ya kasa tsaye, saboda matsalolin da suke kunno kai, ya rasa wanne yakamata ma ya fara ƙoƙarin kawarwa. Kwanaki biyu kenan, ko ya nemi Abdul a waya, baya samunsa. Kuma bai sake zuwa gida ba, hakan ya ƙona wa Indabo rai fiye da kima. Viper bai sake neman Nabila ba, ko a waya, dama bata saka rai ba, dan ta san bata gabansa, idan ta tashi, Walid take kira ta tambaye shi ya jikin Viper, tana ta neman hanyar da zata bi, ta samu ta ganshi, dan sosai Nasir yake sanya mata ido yanzu, ya hanata sakat duk motsinta a kan idonsa, kasancewar motarta tayi damage, an kaita garrage wurin gyara, hatta wurin aiki shi yake kaita, da farko ya so ya Abba ya hanata fitar ma, amma ta din ga kuka, taba nuna wa Abba cewa akwai shari'oin da suke buƙatar ta yi attending. Bayan ya ajiyeta a wurin aiki aƙalla yayi mintuna talatin a tsaye, ko da zata fito, sai da ya samu ɗaya daga cikin security na wurin, ya lambar wayarsa, ya ce masa idan ya ga fitar Nabila ya kira shi ya gaya masa, ya kawo alheri yayi masa sannan ya tafi. Nabila kuwa a office ta iske barrister Habib, ya shirya tsaf zai fita, ta shiga da sallama. Ya amsa mata ya ce "Sannu Nabila, ya hannun?" "Hannu Alhamdilillah, fita zaka yi ne?" Ya ce "Eh, zan je shari'a ne" Ta ce "Mu fita tare, magana nake son mu yi da kai" ya ce "To shikenan babu laifi" suka fita suka shiga motarsa suka fice. Kamar mai aljanu, suna tafe a hanya, ta ce "Ya ajiyeta, tayi mantuwa, office zata koma, ya ce zai kaita ta ce masa a'a, ta fice ta hau napep. Viper ya buɗe ƙofar gidan zai fita, ya ganta a tsaye tana shirin shiga, ta saka hannu ta ɗage niƙabinta, suka yi ido huɗu ya ɗan tsura mata ido, ta faɗa sosai. Ta ce "Ya jiki, ka warware?" "Mmm" "Zuwa nayi mu ƙarasa tattaunawa, ka fara yi mini bayanin shaidun da kake da su a hannu, zan fara gudanar da shari'ar ka, zan cigaba da yi tare da ta ramma, kafin su halaka ni, accident ɗin nan, da nayi, takani aka so yi da mota, garin na kauce musu, nayi accident" ya tsura mata ido, tare da haɗiye wani abu a wuyansa. (Alhamdilillah ala kulli halin, ina godiya sosai da sosai addu'oin da ku ka yi mini, bisa ga rashin lafiya da nayi, Ubangiji Allah ya bar zumunci na gode ƙwarai) Ayshercool 08081012143 70 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cigaba yayi da kallonta, ita kuma ta kasa sake ɗaga idonta ta kalleshi. Yanayinta ya nuna sosai akwai damuwa a tare da ita. "Kin fasa cewar ba zaki tsaya mini ɗin ba kenan?" Ta jinjina masa kai ta ce "Eh, idan ma na fasa, zuciyata ba zata nutsu ba, alƙawari ne da nayi, yakamata na cika, ko ba dan kowa ba, dan wadda aka kashe ba da hakkinta ba" tayi maganar ba tare da ta kalleshi ba. Ya jinjina kai, a hankali ya furta "Ina zuwa" Ya koma cikin gidan, tana tsaye ta bi ƙofar da kallo, ya fito ɗauke da jaka a hannunsa, ya ce "Muje" ba tare da ta san in da zasu ba, ta bishi. Sai da suka yi nesa kaɗan da gidan, sannan ya ja ya tsaya ita ma ta tsaya. Ya samu wuri ya zauna, yayi mata nuni, ita ma ta zauna, ta sauke tata jakar daga bayanta, hannunta ɗaya an naɗa mata bandeji, in da ta samu gocewar ƙashin, sai dai hannun rigarta ya rufe wurin. Ta ciro system ɗin ta, ta ajiye ta ajiye wayarta. Ya zuba mata ido, bai yi magana ba, sai da ta ɗan ɗago ta ce "Wace shaidar da wace shaidar ce da kai, and dan Allah kar ka ɓoye mini komai, saboda kar sai mun je kotu, wani abu da ban san da shi ba, ya taso daga baya". "Me ki ke son sani?" "Shaidunka, da ka ce kana da su" Ya ɗan lumshe idanunsa, sannan ya buɗe ya ce "Madaki, duk na yi masa illa, sai kuma babban yaronsa lakwari, duk suna wurina" "Garkuwa kayi da su kenan?" "Kusan hakan" "Laifi ne fa ka aikata yin hakan" Ya tari numfashinta ya ce "In sake su kenan?" Ta ɗaga idonta, amma taga kallonta yake yi. Jikinta ya ƙara sanyi, maimakon ta mayar da hankali a kan abun da take yi, sai hannunta ma ya hau rawa, wata irin ƙaunarsa ta din ga fizgarta, ji tayi tamkar ta ɗurawa kanta zagi. Ya ɗan matsa kusa da ita, yana kallon fuskar system ɗin ta. Ta takure jikinta, ƙamshin turaren sa da warin sigari suka cika mata hanci. Murya na rawa ta ce "Viper" "Mmm" "Ka sha sigari ko?" Yayi shiru bai bata amsa ba. "Kar ka bari lafiyarka ta taɓu bamu gama shari'ar nan ba, kuma kaga ya fara taɓa maka internal organs, an ce hantarka ta kumbura" Yayi shiru bai yi magana ba, sai kallonta kawai da yake yi. "Akwai abubuwa da yakamata ka gaya mini, amma kamar kana ɓoye mini, yakamata idan kana ɓoye mini ka gaya mini, kar wani abu ya bamu matsala daga baya" Har ta fitar da ran zai yi magana ya ce "Kamar me?" "Suwaye suke goge laifukan ka idan ka yi? Ranar da muka je gidanka, ya aka yi ka gane jami'an tsaro a fararen kaya, har muka tsere musu? Wannan rigar da ka yaga a asibiti ta mecece? Kuma me kake yi da wayata da kake connecting?" Viper ya yi gyaran murya ya ce "Wasu tambayoyin ba su da alaƙa da abun da yake gabanmu, amma na gane jami'in tsaro a farin kaya, saboda ni tsohon mai laifi ne, ba lokacin na fara aikata laifi ba, dan haka duk wani nuƙu-nuƙun jami'in tsaro sai na gano shi. Rigar da ki ke magana a kai, bata da alaƙa da abun da zaki yi a court. Wayarki kuma ina connecting ina duba wasu location, da tura saƙonni. Mai goge laifukana kuma ban sani ba. Sai kuma me?" Nabila ta ce "To shikenan, nan da kwanaki biyu zaka ji ni in Sha Allah, zan har haɗa abun da nake buƙata, saboda yayana ya sakani a gaba da yawa" "Good luck" ya faɗa a takaice, tamkar ta kurma ihu, ko sannu ya jiki bai iya yi mata ba, dan takaici ta tattare system ɗin ta, ta yinƙura ta tashi ta ce "Sai anjima" ya jinjina kai. Jiki a sanyaye take takawa, kamar mara karsashi, ya waiwaya yana kallonta, yadda take ɗaga hannunta tana saukewa, ya tabbatar masa da kuka take yi. Sai da yaji zuciyarsa ta motsa, shi gaba ɗaya tausayinta ma yake ji. Tana tafe a titi, barrister Habib ya kirata, ta ɗaga ya ce "Nabila kina ina ne?" "Meyafaru?" "Wai yayanki yaje ɗaukar ki, an ce masa mun fita, ya kira ni, wai muna ina?" Guntun tsaki ta ja, ta ce "Rabu da shi dan Allah" "A'a kamar yaya na rabu da shi? Kina ina ne, ni ya addabe ni" "Wani wuri naje, ina kan hanyata ta komawa gida, ina son ma ganinka urgent, amma sai Allah ya kaimu gobe" Ya ce "To Allah ya kaimu" Ta amsa da "Amin" *** Naja'atu Bunkure ta dubi Indabo ta ce "A haka ana wannan yanayin zaka koma Abuja?" "To idan ban koma ba yaya zan yi, matsaloli sai kuma cakuɗewa suke yi" "Dole fa a nemo Abdul, kuma ta wani fannin rashin kashe yarinyar nan yayi amfani, amma kuma ya tafka shirme da hauka, dan me zai ɗauketa ya je ya ɓoye, kuma saboda wulaƙanci yaje har gidansu da kansa, dole fa a nemo Abdul ya fito da yarinyar nan" "Kin san ya kashe wayoyinsa gaba ɗaya, kin san a haukan yaron nan ce mini yayi, wai idan ya auri yar party chairman bayan aure zan bari ya auri wadda yake so, kawai ya yi mini wannan maganar, ban sani ba ita yake nufi zai aura ko wata oho" "Taɓɗijan, lallai Abdul wannan karon ya ɗebo ta da zafin gaske, wallahi sai an yi taka tsantsan kafin a warware wannan shirmen da yayi" Indabo ya yakice gumi ya ce "Na rasa makama gaba ɗaya, ga rayuwarsa na cikin hatsari, ya haɗu da mai zamani, wai yaron da ake ta nema ido rufe, shi ne yake yawon sa har da zuwa asibiti, tsoro ma nake ji, kar Vipern yayi masa wani abun" Naja ta ce "Yanzu neman Abdul, shi ne abu mafi a'ala, ina tsoron yayi wani abun da zai tona mana asiri" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ni ɗan da na haifa, nake ta fafutuka a kan rayuwarsa yake neman ya kware mini baya, saboda mace, aishikenan da ina da wata hanyar da zan fito da jafar, da ƙyale shi zan yi, idan abun da yake bi a jikin nata ya gundure shi, sai ya dawo hayyacinsa" Bunkure ta kwashe da dariya ta ce "Barewa bata gudu... A fusace ya kalleta, ta haɗiye dariyar, tana mazewa. *** "Nabila ina ki ka je daga wurin aiki? An ce kun fita da barrister Habib, na kira shi ya ce ba kwa tare. "Eh, uzuri ne ya kamani, na je prison ganin wanda nake karewa ne, ko yanzun ma kana zargin wurin Viper na je?" Kawai ya gyaɗa kai ya fita. Ta kwanta ruf da ciki, ta buɗe wurin da ta ɓoye videon da ta yi wa Viper, ta din ga kallon hotunan da video, tana ƙara jin yadda ƙaunarsa take mamaye zuciyarta. Ta yi shiru, bata taɓa zaton zata tsinci kanta a irin wannan yanayin ba, duk yadda take kallon kanta, a matsayin mai class taga namijin da ya ƙure wa ajinta gudu. Ta dinga shafa fuskarsa, ta kan screen ɗin wayarta, ta lumshe ido tana tuno muryar sa, da a zahiri mai ban tsoro ce, amma a baɗini daɗin sauraro take yi mata, da sanya mata nutsuwa. Ƙarfe takwas da rabi, tana ofishinta, tana jiran barrister Habib. Yana isowa, ta tashi ta tafi, ya ce "Yar ƙwalisa, yaya aka yi ne? Ya hannu" Ta zauna ta ce "Hannu Alhamdilillah, yaya Habib" "Na'am ƙanwa Nabila" "Kamar yadda baka gajiyawa da ni, na sake dawowa neman alfarma a wannan karon" Habib ya ce "To Nabila, me ni ke so?" "Wataƙila wannan ta zama alfarma ta ƙarshe zan neman a wurinka, duk da akwai haɗarin gaske, amma yanzu burikana biyu ne, bayan ganin bayan Bunkure foundation, sai wanke Viper daga zargin da ake yi masa" Da sauri ya ce "Kamar yaya?" "Kamar yadda nake gaya maka, bana nufin na sanyaka a matsala, kamar yadda ka taimakeni kwanaki a kansa, yanzu ma ina neman taimakonka, dan Allah" "Nabila, wannan wasa da rai ne fa, ke ya aka yi ki ka san ba shi da laifi? Tayaya zakinkare mutumin da hukuma take nema ruwa a jallo?" Nabila ta numfasa ta ce "Zaka ga ta yadda zan yi, ni dai haɗin kanka nake buƙata da taimakonka" Ya girgiza kai ya ce "Nabila matana biyu fa da yara uku, haka kurum ki saka su zama zawarawa da marayu, na gaya miki case ɗin sa yayi involving manya haka kurum ki ja mana fitina muna zaman lafiya" Cikin marairaice wa ta ce "Dan Allah yaya habib, ba zan bari sunanka ya fito ba, dan Allah copyn file ɗin sa nake so, da aka yi masa shari'a shikaɗai nake buƙata" Ya ce "Taɓɗijan, ke kin san uban process ɗin da na bi, aka baki ki ka gani wancan lokacin, balle yanzu kicw copy ki ke so" "Dan Allah ka taimake ni barrister Habib" Yayi shiru sannan ya ce "Gaskiya sai kin bani lokaci, dan wanan aiki ne da yake buƙatar ɓoyayyiyar gwagwarmayar " Cikin farinciki ta ce "Zaka nemo mini ɗin? "Zan jarraba ne na gani idan zai yiwu, ba alƙawari nayi miki ba" Ta miƙe cikin farinciki ta ce "Na gode sosai, Allah ya saka da alkhairi ya raya zuriya" Ya amsa mata da Amin. *** Ramma tana ta gogewa Abdul labcourt ɗin sa, ya daɗe a tsaye yana kallonta, wani irin matsanancin tausayinta ne ya mamaye zuciyarsa. Ya ƙarasa ya zauna ya ce "Rahama" ta ɗago ta kalleshi. "Ina da masu gugu fa, kaiwa nake yi ayi mini, ki ke wahalar da kanki" "Ka ce zaka yi tiyata, shiyasa nake goge maka" Yayi murmushi ya ce "Ai ba da labcourt muke shiga tiyata ba, kayan tiyata daban suke" Ta ce "Ok, duk da haka ka saka wani lokacin" Ya jinjina kai ya ce "Rahama menene babban burinki a rayuwa ne?" Ta sunkuyar da kai ta ce "Ka mayar da ni wurin mamana" "Na san da wannan, zan mayar da ke, burinki na rayuwa?" Ta ɗago idanu ta kalle shi ta ce "Babu" Ya ce "Kamar yaya? Kowane ɗan Adam yana da buri da yake son cimma a rayuwarsa" Rahama ta kashe socket, ta kalleshi ta ce "Wace rayuwar? Rayuwar da ka gama kassarawa wane buri ne yayi mini saura? Ka mayar da ni wurin mahaifiyata na ƙarasa rayuwata shikaɗai ne roƙona a gareka, amma ba ni da wani sauran buri da nake da shi, gaba ɗaya rayuwar ta fita daga raina, babu abun da yake burgeni yake bani sha'awa". Abdul ya koma kusa da ita ya zauna, ya ɗan tsura mata ido, ita kuma ta kawar da kanta gefe ɗaya. "Dukkanin mai rai baya fitar da rai, da cimma burikansa na rayuwa, na san ni ne musababbin rushewar naki, amma haryanzu ina dana sanin abun da na aikata, amma zan cika miki burinki Rahama, zaki koma makaranta kiyi karatu mai zurfi in dai muna tare in sha Allah, makaranta mai kyau zan mayar da ke, na gyara makarantun garinku, kuma an karɓi ƙudurin gyaran hanyarku, aiki yayi nisa na yi muku boreholes kamar yadda nayi miki alƙawari, idan aka kammala zan nuna miki" Maimakon ta yi magana, kawai sai ta fashe da kuka. Cikin damuwa ya ce "Rahama menene kuma?" "Ni duk bana son wannan abubuwan, kawai na koma gidanmu na ƙarasa rayuwata, babu wani abu da zan zama a rayuwa da zai katange ni, daga tsangwamar da zan fuskanta a cikin al'umma, wannan ɗabi'a ce ta hausawa" "Ina tabattar miki da idan muna tare, babu wanda zai tsangwame ki, wasu shirye shirye nake yi ne, da sun tabatta in sha Allah zamu je ki ga mama, amma babu maganar rabuwa tsakaninmu, ba sai na bar ki a tsakanin hausawan ba ma zau yi miki, ki daina damuwa Please bana so" Wayarsa ce ta fara vibrating, ya ɗaga ya ce "Yeah Salim ya ake ciki ne?" "Wai ina ka shiga ne? Mummy ta kira saifu a waya, wai an nemeka a waya an rasa, ya ce mini shi ma baya samunka a waya, ni kaina kwanana biyu kenan ina nemanka yanzun ma ban zaci zan sameka ba, nace bari na jarraba kiran wannan layin naka" Abdul ya numfasa ya ce "Akwai damuwa ne Salim, mu haɗu a gidana na by pass" "To shikenan, ka san nina har ta gaji da nemanka ita ma, har clubs ka daina zuwa, gidanka da take samunka ma yanzu baka zama, kuma ta daina samun wayarka, na ce mata kayi busy ne da shirye shiryen siyasarka" Abdul ya ce "Manta da ita, zan je asibiti zan yi tiyata da daddare, idan na kammala ko kafin na tafi, sai mu yi magana sai mu haɗu" "To shikenan, sai na ji ka" *** Walid ne ya ƙarasa in da Viper yake a zaune a kan dutsen nan, yayi shiru yana nazari. Ya zauna a kusa da shi ya ce "Sannu da hutawa" "Yauwwa sannu da zuwa" "Yauwwa, tunanin me ka ke yi ne?" Viper bai ba shi amsa ba ya ce "Meye labari?" "Labari, yan unguwar su madaki, sun addaba wa yan unguwarmu, naji ɗan mama ya ce zai shiga unguwar, sai kuma na je maɓoyar madaki, na tarar baya nan, ko dai ya tafi wani wurin bamu sani ba?" Viper ya ɗan kaɗa kai ya ce "Kar ka damu na san in da yake" Cikin mamaki ya ce "Ka san in da yake kamar yaya?" "Kamar yadda na ce" ya faɗa a taƙaice. Shiru ya wanzu na wani ɗan lokaci, Viper ya ce "Jibi yarinyar nan zata shiga kotu, ta kuma ce a kwankin nan zata fara shari'ata, i need to assist her, a haka ma rayuwarta na cikin hatsari, muddin ta shiga case ɗin nan matsaloli zasu ninku fiye da baya, akwai buƙatar na taimaka mata sosai" Walid ya ce "Haka ne, Allah ya tabattar mana da alkhairi, ya bamu dukkanin nasara, ka yi yanci mai zamani, ka daina wannan zaman ɓuyan" Viper ya dafa kafaɗar Walid ya ce "Mai laya" "Na kiyayi mai zamani" "Mu huta wannan zaman ɓuyan zaka ce, idan Allah ya bamu nasara, in ga kun tsaya da ƙafafuwan ku, na aurar da kai, da wancan sarkin faɗan" Walid ya ce "A'a, ka yi yanci, muga farincikinka da walwalarka sun dawo dai, mu dai mu cigaba da gurgura rayuwa" Viper ya girgiza kai ya ce "Aure yana da daɗi mussaman idan ku ka yi dace kamar yadda na yi. Ni na taɓa yi na more shi, kuma yakamata ku yi, idan na bari ku ka ƙarar da rayuwarku a kan hidimata kawai ban yi wa kaina adalci ba muhsin" Walid ya ce "Taɓ anya na taɓa jin ka kira ni da ainihin sunana kuwa?" Viper ya yi murmushi ya ce "Ka tuna mini da watarana, da 'yar madara ta sakani a gaba, ta ce sai na gaya mata ainihin sunayenmu, na ce mata ni Muhammad Al'amin, kai Muhsin, liti Abdullahi. Ta rafka salati, ta ce kalli yadda duk kuka mayar da sunayenku wani iri, har ma ɗan gara yaya walid, duk da shi ma wataran mai laya kake ce masa, gaskiya ku canza hali, sunayenku masu daɗi, amma duk kun canzawa kanku suna. Na ce ;Sunan waye yafi daɗi, tayi murmushi ta ce na mijina, na ce yauwwa ke ma sunanki mai daɗi an saka miki wani iyayi daban. Muhsin ku yi aure akwai alfanu a cikin aure, haryanzu na kasa manta rayuwar cikin aure, na san abu ne da ba zai bar ƙwaƙwalwata ba. Ina son naga kun samu cigaba a rayuwar ku, ba zan yi alfahari da ku ƙarar da rayuwarku a kaina ba" Walid ya kalli Viper ya ce "Al'amin, ko mai muka yi maka a rayuwa ka cancanta, ai duk ɗan halak baya manta alkhairi, idan kai ka manta ni ba zan manta ɗawainiyar da ka yi da ni da mahaifiyata ba, haka zalika mutuntawar da matarka tayi mana" "Muhsin, mahaifiyar ka, mahaifiyata ce, ka daina saka wannan a lissafi" Walid ya ce "Na daina, amma dai sai mun fara aurar da kai tukuna, farincikin ka da walwalarka su dawo, sannan mu san abun yi mu ma" Viper ya girgiza kai ya ce "Bani da ra'ayin kuma yin aure a rayuwata, wancan ma tsautsayi da ƙaddara ne ya saka aka yi shi" Walid ya yi murmushi ya miƙe ya ce "Wannan kuma, ƙaddarar tausayi da soyayya zai saka a ayi shi" har Walid ya yi gaba, Viper ya miƙe da sauri ya ce "Ina ba zai yiwu ba, jauhar ce kawai a zuciyata" kawai walid ya ɗaga masa hannu ba tare da ya waiwaya ba ya yi gaba yana dariya. *** Salim ya kalli Abdul da ya shigo a gajiye, ya zauna ya ajiye labcourt ɗin sa a gajiye. "Yaya ne mutumina, na ganka a wahale" "Aiki na sha yau ɗin nan, na je asibiti ya kai huɗu, na duba wanda na yi wa tiyata, sannan na yi wa wasu aikin sai godiyar Allah" Salim ya yi murmushi ya ce "Sannu, ko in ɗaukko maka abar ne, ina da ita a mota?" Abdul ya girgiza kai ya ce "Rahama ta san warin giya, faɗa zamu yi da ita" Salim ya ce "Wow, to ko abinci zamu je ka ci?" Nan ma ya girgiza kai ya ce "Ina da special cook a gida, yarinyar nan dar ce" yayi maganar yana kashingiɗa. Salim ya kwashe da dariya ya ce "Allah mutumina, ta saduda kenan?" Abdul ya yi murmushi. "Ina jinka, bani labari" "Salim, kai ka san komai, tun da ka tafi fa babu labarin mahaifiyar yarinyar nan, gashi ta matsa mini na mayar da ita gida, ni ba mayar da itan ne ya dame ni ba, na fara yi wa daddy bayani ko zai fahimce ni, ya hau ni da faɗa da zagi, kuma wai lallai sai na kai masa ita, sai an kaita kotu ta bayar da shaida, ni fa na yanke shawarar zan ɗauke ta mu ƙara gaba, har takarar ma bana so. Wallahi Salim ban taɓa dana sanin aikata wani abu a rayuwata ba, irin yi wa rahama fyaɗe ba, kuma ban taɓa jin so da ƙaunar wani abu a raina ba, kamar yadda nake jin son ta, ya mamaye zuciyata ba, Salim wallahi ba zan iya rabuwa da rahama ba, ba wai ina sonta da jikinta ko wani abu ba, ita ɗin nake so" Salim ya ce "Ƙarya ne malam, mun san komai fa" Abdul ya yi murmushi ya ce "Ita ta sani ai, ba zan yi maka ƙarya ba" Salim ya ce "Kar ka damu, na fahimta maganar ka ɗauketa kayi gaba bai taso ba fa, ka zauna ka yi wa daddy cikakken bayani" "Salim na san waye mahaifina ciki da bai, muddin na fito da rahama, zai iya salwantar da rayuwarta, ita kanta mahaifiyarta ina tantama a kan bashi ne ya ɗauke ta ba, ni kuwa a kan rahama sai dai ayi duk wadda za ayi" Salim ya waro ido ya ce "Da iyayen naka? Abdul yaushe ka koma haka ne? A cikinmu duk rashin nan da kai da Saif kun fi mu mutunta iyaye ma da jin maganar su mussaman kai, meyasa ka ke son canzawa saboda mace?" "Kamar yadda take yawan faɗa, na riga na ɓata rayuwarta, dan haka ba zan bari a sake tagayyara rayuwarta ba, ina son rahama irin son da nake son na ƙarasa rayuwata da ita, idan Daddy ya cigaba da matsawa, ba zan yi wancan auren ba" Ya girgiza kai ya ce "Ba za ayi haka ba, ka je ka fara maganar da mahaifiyar ka, ko zata fahimceka" Ya ce "Taɓ ayi sha'ani kawai, zan je zanji kiran da yake yi mini amma in fito da rahama dai, gaskiya ban ji zan iya ba" "Amma fa Abdul mun tafka shirme a gaban uwar yarinyar nan, anya zata yafe maka kuwa? Ga tsiyar da ka je ka kuma yi daga baya" Abdul ya numfasa ya ce "Sharrin giya ne, da gigin arziki da nake ji da shi, nake jin kamar zan iya taka na ƙasa da ni, ni komai zata yi, mini tayi mini amma ban da raba ni da yarinyar nan". Salim ya ce "Lallai ka faɗa da yawa mutumina" "Rahama, akwai haƙuri, duk da ina cin zagi a wurinta da tsinuwa, amma da ta ganni cikin rashin lafiya, ko damuwa hankalinta yake tashi, ita take dafa abincin da zan ci, yau har da yi mini guga. Nifa yarinyar da aka ce za a haɗa ni da ita, gaba ɗaya bata yi mini ba buɗaɗɗen ido ne da ita, gara a bar ni da rahaman dai, na san koma menene ni ne sila" Salim ya jinjina kai. *** Nabila ce a tsaye a gaban court, tana ƙoƙarin fara gabatarwa da mai shari'a appeal ɗin su, ta kalli barrister Habib, ya jinjina mata kai alamar bata ƙwarin gwiwa, ta tsaya ta gabatar da kanta cikin harshen turanci, tare da fara karantowa kotu koken su. Na kotun ta yi duba da rubutaccen jawabin da suka gabatar, a kan hukuncin da kotun farko ta yi, bisa ga wasu kurakurai da suke ganin an tafka a wurin yin shari'ar, na rashin bayyanar wadda abun ya faru da ita a gaban kotu, da rashin gabatar da medical report ta hannun ɗan sandan da kuma likitan da ya tabattar da yin laifin ba. Hakazalika a hujjojin da suka gabatar a kotun farko, akwai sautin murya, na mahaifiyar ramma tana koken a kawo mata agaji, domin kuwa wanda ya yi mata fyaɗe ya dawo ya ɗauke ta, idan kuwa haka ne, wanda ake zargi ba shi ne ya aikata wannan laifin ba, sannan kuma wanda ake zargin ya amsa laifin ne, a sakamakon barazana da aka yi masa, da haka take roƙon kotun ta bibiyi shari'ar da kotun baya tayi, ta tabattar da adalci" Ta miƙa file ɗin aka miƙa gaban mai shari'a. Suna tafe a mota tare da barrister Habib ta ce "Yaya, gaba ɗaya jikina a sanyaye yake, gani nake wannan karon ma, ba zan yi nasara ba" "Bana son saurin karaya dan Allah, kin manta wadda ki ke ƙoƙarin tunkara ta fi wadda ki ke yi yanzu? Kuma yanzu hankalin mutane da yawa ya dawo kanki, ba common mutanen gari ba, har da ma'aikatan shari'a" "Idan Allah ya sa na yi nasara, akwai gagarumin tonin silili fa" tayi maganar tana murmushi. Barrister Habib ya kalleta ya ce "Na me fa?" "Zaka gani kai dai, ya batun case ɗin Viper, samo mini copyn shari'ar da na ce?" "Ai na gaya miki ba aiki ne mai sauƙi ba, ina nan ina ƙoƙartawa, yanzu idan aka san ina ƙoƙarin samo file ɗin ma, rayuwata na cikin hatsari" Ta jinjina kai ta ce "Haka ne, Allah ya ba da sa'a" *** "Inadabo, wallahi akwai matsala muddin Abdul bai kawo yarinyar nan ba, tun da ya ce maka tana wurin sa ya fito da ita mana" "Naja duk wani ƙoƙari ina yi, bai taɓa bujirewa umarnina ba sai a wannan karon, yama daina zuwa in da nake gaba ɗaya, bana samun wayoyinsa" "Ka san kuwa me nasararta a appeal ɗin nan yake nufi? Yarinyar nan fa ba zata zuba mana ido ba, dole ka yi ƙoƙari fa a kai" "Kar ki damu, zan ga alƙalin da kaina" Bunkure ta girgiza kai ta ce "Ƙoƙarin ka ba a kan alƙali kawai zai tsaya ba, har da wannan yarinyar, dan ni na yi iya yi na" Inadabo ya katse kiran, ba tare da ya sake yin magana ba. **** Babu tsammani, indabo ya shiga falon mai ɗakinsa, ya tarar da ita tana yi wa Abdul faɗa. Yayi turus, sannan cikin tsananin ƙuluwa ya ce "Ai dama na sani, ke ki ke goya masa baya, yake rashin mutunci" "A'a nima fa yanzu na ganshi, nake tambayarsa ba'asin ina ya shiga, kar ma ka ɗora mini wannan zargin" "Wato Abdul ban isa da kai ba kenan ko? Nayi maka magana sai ka ɗauke ƙafarka gaba ɗaya daga gidan ka daina zuwa, ina yarinyar take?" Abdul ya yi shiru ya ƙi magana. "Ka gaya mini in da take, tun ban tattaka ka ba, yau an yi appeal ɗin shari'ar yarinyar, kuma muddin aka wanke mutumin nan, babu lallai ka tsira ba tare da asirinka ya tonu ba". Abdul ya ce "In dai hakan yana nufin na cigaba da rayuwa da ita, shikenan ni ba komai asirin nawa ya tonu, dan Allah Daddy ka yi haƙuri, wallahi ba zan iya fito da rahama gaban duniya ba, ban san iya abun da zaka yi mata ba, kuma bana fatan abun da zai ƙarasa zubar da mutuncinta, dan kuwa fito da ita gaban kotu kamar cigaba da yayata abun da ya faru da ita ne" Tamkar shashasha indabo ya tsaya yana kallon Abdul, babu kunya babu tsoron Allah Abdul yake gaya masa wannan maganganun. Ya numfasa ya ce "Babu laifi, ni na san matakin da yakamata na ɗauka". *** Nabila ta shiga office ɗin ta, ta zauna ta janyo drower zata ɗauki biro, ta ga file, ta ɗaukko file ɗin ta buɗe, kawai taga copyn shari'ar Viper ne a ciki, sai da ta razana ta ja da baya, tana waige-waige. A razane ta ɗauki waya, ta kira barrister Habib, ya ɗaga ya ce "Hello Nabila" "Barrister ka samo file ɗin nan ne?" "A'a, ina ta ƙoƙari dai a kai, ki yi haƙuri" "Barrister, file ɗin na gani a office ɗina" Ya ce "Wane file ɗin?" "Na shari'ar Viper" "Iyee, waye ya baki?" "Nima ban sani ba, a office ɗina na tarar kamar yadda aka ajiye mini na Bunkure" "Kar ki gaya wa kowa, gani nan zuwa" Ta ajiye wayar tana sake dudduba file ɗin. Ji ta yi an buɗe ƙofar office ɗin ta razana da sauri tana ɓoye file ɗin, ya rufe ƙofar office ɗin, ya ƙaraso. Ta ce "Yau ma kai ne da kanka?" Ya ce "Eh, ko in koma ne?" "A'a, bisimillah zauna" Ya samu wuri ya zauna, kamar yadda a wancan karon, tayi masa hidima, haka ma a wannan karon, ta haɗa masa tea, ta bashi abincinta da ta zo da shi, ta bashi" wannan karon babu gardama ya karɓa ya ci. Ta ciro file ɗin ta ajiye masa ta ce "Yau da safe aka kawo mini shi, ban san kuma wanda ya kawo ba" Ya karɓa ya bubbuɗe, yana dubawa. "An fitar da sanarwar cigaba da nemanka jiya, wai yaranka sun je sun yi faɗan daba, jami'an tsaro na ta cigaba da yayata nemanka" Ya girgiza kai ya ce "Ni ma na ji, sai dai ni bani da masaniyar hakan, na samu labarin faɗa tsakanin yan unguwarmu da yan unguwar su madaki, ban san ma me ake ciki ba" "Zan je kotu, na nemi kotu ta hana kama ka, kafin na ɗauki mataki na gaba" Viper ya jinjina kai yana kora shayin hannunsa. Ya ce "Bani system ɗin ki" Ta ɗaukko, ta bashi ya ciro tab ɗin sa, ya ɗan jima yana danne-danne, yayin da ita kuma take satar kallonsa kamar yau ta fara ganinsa. Kamar kar ya tafi ta daina ganinsa, wani irin shauƙi da farinciki ya din ga ratsa zuciyarta. "Ki shirya, zamu je ki ga shaidar da nake da shi, idan da abun da ki ke buƙatar sani" Ta ce "To shikenan, ka sanya lokaci sai mu je, sai kuma mu yi ta addu'a". Ya ɗan daddana tab ɗin hannunsa ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Barka da wannan lokaci, kana magana da mai zamani ne. Babu buƙatar yin doguwar magana, na san zuwa yanzu ka san labarin haɗuwata da ɗanka, zuwa yanzu na san duk wani motsinsa, duk in da yake zuwa na sani, amma ba wannan ba, akwai buƙatar ka bibiyi case ɗin ɗanka da ka ke musayar sa da ni, a lokacin da yake Nigeria yake aikata laifuka, ina da babban albishir gareka, Mexico na shirin miƙawa amurka shi, ya fuskanci shari'a, kuma ina mai sanar da kai kisan kai ne hukuncin abun da ya aikata. Na san zaka yi mamakin yadda aka yi aka kama Jafar, akwai buƙatar mu haɗu fuska da fuska nayi maka bayani" ya katse wayar, tare da tashi tsaye ya ce "Ka zan bar wurin nan" Ita ma ta miƙe ta ce "Amma.... "Amma me?" Sai ta tsaya tana kallonsa "Ina son mu yi magana ne, ina da tambayoyi" "Ba yanzu ba, am not safe here" Ta ce "To muje, na raka ka gate nima fita zan yi" ta tattaro file ɗin, da jakarta suka fito. Tun kafin su ƙaraso, ya zuba masa ido, duk da fuskar Viper sanye yake da facemask, amma hakan bai hana shi gane ko waye ba. Suna ƙarasowa yayi murmushi ya ce "Barrister, wurinki na zo, ina Abuja aka ce mini kin samu accident, sai dai na samu labarin da sauƙi jikin, duk da haka na ce bari na zo na ganki, kuma na ganki da baƙo. Assalamu alaikum" yayi maganar yana miƙawa Viper hannu. (Ayi mini afuwa ji na shiru, bani da lafiya ne) Ayshercool 08081012143 71 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Viper ya tsaya ƙyam yana kallon Alhaji mu'azzam da ya miƙo masa hannu. A rikice Nabila ta ce "Amm eh, ai na ma warware na ji sauƙi, ka shiga, ka jira ni a office ɗina, yanzu zan dawo" Viper ya kalli Nabila ya ce "Koma ciki" sai ta tsaya tana rarraba ido, tana kallonsa tana kallon Alhaji mu'azzam wada. Wani irin kallo Viper ya yi mata, da ya tilasta mata barin wurin, tana waiwayawa. Viper ya saka hannunsa a hannun Alhaji mu'azzam, ya sauke facemask ɗin sa yana kallon cikin idonsa. "Dama ana ganinka, ka yi wa hukuma wuyar kamawa? Ya aka yi na ganka tare da yarinyar da nake so, kuma nake fatan na aura?" Viper ya tsananta riƙon da ya yi wa hannun Alhaji mu'azzam ya ce "Ka gaya mata wani abu ne?" "Kamar me fa?" "Ka san abun da nake nufi" yayi maganar yana ƙara tsare shi da ido. Alhaji mu'azzam ya ce "Kana tsoron wani abu ne?" "Ba maganar tsoro bane ne ko akasin haka, gargaɗi ne nake yi maka, idan baka furta ba kar ka fara, nike da alhakin kai ƙarshen wannan lamarin, idan ka yi wani yinƙuri da zai kawo tangarɗa ga abun da nake tsarawa, ka san abun da zan iya aikatawa". Alhaji mu'azzam ya yi murmushi ya ce "Da fari jauhar, na bar maka ita, a wannan karon kuma Nabila, kar ka zama mai...... "Jauhar ta wa ce, haka zalika Nabila, muddin zan cigaba da ganin fuskar jauhar a cikin ta Nabila ta haramta a gareka, ba kai ba kowane mahaluki ma" ya fizge hannunsa daga na Alhaji mu'azzam ya mayar da facemask ɗin sa ya bar wurin. Nabila kuwa kai komo ga din ga yi a office ɗin ta, cike da fargaba da tsoro. Kankarofi ya turo ƙofar office ɗin Nabila ya shigo, ta tsaya tana kallonsa yayi mata murmushi ya ƙarasa ya ce "Madam ya na ganki a tsaye ne?" Murmushin ƙarfin hali ta yi ta ce "Bisimillah zauna mana" Ya zauna ya ce "Ashe tsautsayi ne ya kuma afkuwa haka, ya ƙarfin jikin?" Ta ce "Jiki da sauƙi Alhamdilillah" "Amma dai babu wani mummunan rauni ko?" Ta ce "Eh, gocewar ƙashi na samu a hannuna, amma Alhamdilillah da sauƙi" "To Alhamdilillah, na ji daɗi ƙwarai, ya shari'a kuma?" Tayi murmushi ta ce "Mu na ta fama, sai fatan Ubangiji Allah ya iya mana" "Allah ya yi jagora, kin ga kamata yayi ace har gida na je dubiya, daga nan na miƙa buƙata ta ga Abba, ayi komai a kan lokaci, kin ga babban mutum ne ni, amma soyayya ta saka sai wahalar da ni ki ke yi, kina sakani sintiri, sai dai na yi ta biyoki office" Ta ɗan shagwaɓe fuska ta ce "Wahalar da kai kuma?" Ya kwantar da murya ya ce "Eh mana, ko ba ayi na ne, ya sanya ake ta bani wahala" "Matanka fa biyu, ni gaskiya... "Ba kya son mai mata ko?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "To meyasa?" "Wahala ake sha, kuma nan da nan ake sakin wadda ta zo daga baya, impact ni fa tashin hankali ne ba na so, gidanmu ma uku ne, ina ganin tashin hankalin da ake yi" Yayi dariya ya ce "Barrister, dabarar mutum ba ta sanyawa ya kaucewa ƙaddararsa. Da dabara da wayon mutum na sanyawa ya kaucewa ƙaddara, da wataƙila haryanzu fatima tana raye da ni ta aura" "Wacece hakan?" "No kar ki damu, kawai dai misali nake yi miki, wata yarinya ce da na taɓa ƙallafa raina a kan aurenta, Allah bai yi ba" "Baka aureta ba, sai ka auri mata biyu, yanzu da sai ka yi ta uku da ita ni ta huɗu?" Sosai ta bashi dariya, saboda yarinyata da kishinta da suka gaza ɓuya. "Karki damu, labarin ne akwai sarƙaƙiya, idan ya zo ƙarshe zan baki. Amma matana ba matsala bane. Uwargidana tana Abuja, amaryata kuma na kano, ke kuma sai in da ki ke so zaki zauna" Noƙe kafaɗa tayi, tana ɗan tura baki, har ya gama yi mata hirar, bai yi mata magana akan Viper ba, duk da ta so ta tambaye shi ko ya san shi, amma ta ja bakinta tayi shiru, dan da Viper yakamata su tattauna wannan maganar. **** Naja'atu Bunkure ce zaune a office ɗin Abdul yasar, ya hakimce a kan kujera yana saurarenta. "Abdul, yarinyar nan fa dole ka fito da ita, even for your own safety, idan fa aka wanke mutumin nan, akwai cakwakiya, bamu san ya shari'ar nan zata kasance ba, taurin kan nan da kake yi, babbar barazana ce gareka da mahaifinka Shari'a saɓanin hankali ce" Abdul ya ce "Ba wata barazana, ai ba yau ki ka saba goge laifi ba komai girmansa, wannan karon ma ki yi wani abu" "Nayi iya yi na, da kai da mahaifinka ne kuka ɓata komai, Abdul idan lamarin nan ya kwaɓe fa, zaku shiga matsala mussaman ma kai. Kuma an gaya maka shaida kawai zata bayar a kotu shikenan ba wani abu ba" Abdul ya yi murmushi ya ce "Naja'atu Bunkure, na sanki fa, na kuma san waye mahaifina, na san abun da zaku iya na san wanda ba zaku iya ba. Idan aka kuma cutar da yarinyar nan a karo na biyu, ba zan yafewa kaina ba, ke da kanki kin san kura tayi lafiya, duk da a duk lokacin da zan shiga Asibiti ina ajiye duk wani iskanci a gefe, in shiga a nutse, amma ke kin san yanzu na nutsu sosai da sosai, albarkacin rayuwa tare da rahama" Naja ta tafa hannu ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Abdul kidnapping fa kenan, bayan fyaɗe ka saceta kana rayuwa da ita, wani laifin fa kake aikatawa a kan wani" "Babu wani laifi da nake aikatawa, da na barta to da tabbas kun yi mata wata illar, barinta a wurina shi ne zata zauna safe" "Shikenan, zamu ɗauki duk wani mataki da hukuncin da muke ganin ya dace" Ya ɗage kafaɗa alamar ko a jikinsa. *** Indabo kuwa gaba ɗaya ya kasa zaune ya kasa tsaye, ya rasa abun da yake yi masa daɗi, tun yana ƙirga adadin shigarsa banɗaki, har ya sare lissafi ya ƙwace masa. Gudawar tsoro da fargaba kawai yake yi, tun bayan da Viper ya kira shi a waya. Embassy ɗin Nigeria na Mexico ya kira, domin a bincika masa da maganar da Viper ya kira shi ya gaya masa, idan gaske ce. Ya ma rasa wa zai kira ya gaya wa maganar, ashe da gaske yana sane da cewa, da shi yake sakawa ayi exchange a duk lokacin da jafar ya aikata laifi, to ko da sanya hannunsa aka kama masa ɗa? Amma ya za ayi common ɗan daban gari, ya saka a kama masa ɗa a ƙasashen ƙetare?. Waya ya ɗauka ya kira IG, ya din ga masifa, a kan jan ƙafar da ake yi, wurin kama Aminu Viper, tare da jadadda idan har ba za su yi abun da yake so ba, zai shiga ya fita a ɗauke shi daga garin kano, a canza wani IG. Tun da suka kasa kama mutum ɗaya, alhalin yana yawonsa a gari, da aikata abun da yake so. Yayi ta bashi haƙuri, tare da bashi tabbacin suna iya ƙoƙarin su, amma komai ya kusa zuwa ƙarshe. Ya ajiye wayar yana mamakin ya za ayi, ace senator guda ya tayar da hankalinsa haka a kan ɗan daba guda ɗaya tal har haka, ya din ga ɓata lokacinsa a kansa. Yadda indabo ya kira shi, ya tayar masa da hankali, haka shima ya kira Nasir a waya, ya ce masa nan da kwanaki talatin, idan babu improvements a aikin nan, zasu karɓi aikin daga hannunsa su bawa wani, kuma hakan ka iya janyo masa demotion, da rasa wasu damarmaki. Shi ma haƙurin ya din ga bayarwa, tare da bada tabaccin zai kama Aminu Viper. *** Abdul da la'asar ya koma gidansa,ya tarar rahama na wanka, ya kwanta ya yi ɗai-ɗai a kan gado. Ta buɗe ƙofa ta fito, ta tarar da shi ta ɓata fuska ta ce "Abdul meye haka?" Ya buɗe ido ya kalleta. "Na gyara gadon, kawai ka hau ka ajiye mini shirginka, wata uwar jaka kamar wanzami, kalli takalmi har bedroom ba a wancan ɗakin nake ajiye maka ba? Lumshe idanunsa ya yi, ta ƙarasa ta kwashe kayan, ta hau kan gadon ta kwance agogon hannunsa, dan ta san ƙarshe ya cire, ya yar da shi a wani wurin, ya zo ya isheta da nema. Ya kai hannu ya fara shafa bayanta, tayi masa banza, tana cikin ɓalle masa labcourt ya cigaba da shafa gashin kanta, sai da ya kai hannunsa kan towel ɗin ta, ta buge hannunsa da ƙarfi ta ce "Tashi kayi sallar la'asar na san baka yi ba" ya buɗe idonsa ya kalleta. "Eh kana wani manne ido, ka tashi kayi sallar la'asar" "Zan yi in anjima, yanzu na gaji" Ramma ta buɗe baki ta ce "Wace anjiman? Kai ke da anjiman? Waye ya baka guarantee kai wa anjiman? Abdul wallahi wutar duniya ma ba zaka iya da ita ba, balle ta lahira, kai a wuta kala nawa kake so a saka ka ne? Saƙara fa, wutar marasa yin salla, ita ka ke so ka shiga ko? bayan ta shan giya da neman mata. Ba shiri ya tashi ya ajiye labcourt ɗin ya ce "To naji, ai dama ban ce ba zan yi ba, zan yi Astagfirullah in sha Allah ba zan shiga wuta ba, shan giya da neman mata ai kin san na daina" yana maganar ya nufi banɗaki. Sai da tayi dariya, Abdul ga tsoro ga iskanci, ta tabatta da ya samu kyakkyawar tarbiyya, da isashshen ilimin addini, da bai aikata wasu abubuwan ba. Taje gaban mudubi ta zauna, mudubin fal da turaruka, da kayan gyaran gashi da na fata, wasu abubuwan duk shi ya koya mata amfani da su, har wasu supplement yake bata tana sha. Ita kanta ta san tayi ƙiba ta yi kyau. Tayi ajiyar zuciya ta fara shafa man. Ya fito ya tayar da salla, ta ce "A kyautata niyya da nustuwa idan ana salla, yadda ka yi ta haka zata zo maka a kabari" ta shirya cikin doguwar riga, yana idar da sallar, ta ɗaukko masa azkar ta ce "Ungo, ka san shi yawan ambaton Allah, yana hana mutum aikata alfasha, abu ne mawuyaci kaga wanda yake da kusanci da Allah, yana aikata ɓarna kala-kala" haka ta saka shi a gaba, ya idar suka je ya ci abinci. Gaba ɗaya rayuwa da ramma ya sanya ya ji tamkar an canza shi, zuwa wani na daban, haka kurum yake jin wata nutsuwa a tare da shi. Mussaman saita shi da take yi a kan ibada, da yawan tsoratar da shi a kan yin ta, haka yana saka masa nustuwa da kwanciyar hankali, kuma ya rage aikata tsageranci da rashin ta ido. Hakan ya sanya yake ƙara jin raba shi da ramma, tamkar raba shi da rayuwar sa ne. System ya kunna ya ce "Your excellency zo ki ga wani abu" "Wanke-wanke zan yi na ɗora abincin dare" "Karki damu, zan yi mana takeaway" "Sai dai idan zaka yi wanke-wanken" Abdul ya ce "Na ji zan yi" Ta ƙaraso ta zauna, ya rungumeta a jikinsa, sannan ya buɗo wani form ya ce "Kin san na menene wannan?" "No" "Form ɗinki ne na makaranta" Ta kalleshi ta ce "Makarnta kuma?" Ya ce "Eh mana, ko ba kya so?" "Ina so, amma gida zaka mayar da ni?" "Eh, zaki je ki ga gida, daga nan sai school, boarding ce, mai kyan gaske, saboda sonake ki nutsu ki yi karatu da kyau, yadda babu wanda ya ganki, balle yayi miki gori, da kin gama karatu kuma, ƙasar waje zaki tafi jami'a, shiyasa nake tambayar ki me ki ke son zama, na biya komai, na yi rubutu, yadda ko bayan raina ba zaki tozarta ba in sha Allah, ko bana raye karatunki ba zai tsaya ba sai kin kammala in sha Allah" "Yar uban wace ni da zaka yi mini duk wannan hidimar haka?" "Ba yar kowa ba ce, amma komai zan yi miki, ba zai kai nauyin laifin da nayi miki ba, ba zai biya budurcinki da na karɓa ta ƙarfin tsiya ba, da kuma rashin darajar da naje gidanku nayi ba, ba zan gaji da cigaba da neman afuwar ki ba rahama" ta sunkuyar da kai ta yi shiru, hawaye na zubowa daga idanunta. Ya saka hannu yana share mata hawayenta ya ce "Ki yi haƙuri, na san na cutar da ke, dan Allah ki yafe mini rahama, soyayyar nan kawai da Allah ya jarabbe ni da ita, ta isheni, baki san tarin ƙalubalen da yake a gabana nake ta ƙoƙarin karewa a waje ba, amma dai ki yi haƙuri dan Allah" a hankali ta zare hannunta daga nasa, ta tashi ta bar falon tana kuka. *** Nabila kuwa da file ɗin Viper ta tafi gida, ta kai shi ɗakinta, ta cigaba da duba shi daki-daki, tana picking ɗin kurakuran da aka tafka a cikin shari'ar ta sa. Kai da ganin fasalin shari'ar ka san cewa cike take da mugunta da zunzurutun zalunci. Zafi ne ya isheta, babu wuta, ga solar sai ƙara take yi, kasancewar ranar ba ayi rana sosai ba. Ta ɗaukko system ɗin ta, da wayoyinta, ta fita gareji, ta shimfiɗa sallaya, da kayan ciye-ciyenta, ta zauna ta cigaba da aikinta. Nasir ne ya fito yana waya, ba ta san da wa yake yin waya ba, sai dai yanayin yadda ya fito yana wayar, bai san tana wurin ba. "Eh dan Allah, duk yadda za ayi a samo mana hotunansa, ko guda ɗaya ne, nima na daɗe da wannan tunanin, ban aiwatar ba, amma a yanzu naga hakan ne kawai mafita, a samo hoton nasa, dan IG ya kira ni ɗazu, shi kansa distinguish sai da ya kira ni, ni duk na ruɗe, nayi mamakin yadda aka yi mutum ɗaya ya gagari hukuma. Duk wata hanya da na bi da zan sameshi, sai ta kuɓuce mini. Shiru ya yi, lokacin da ya lura da ita a wurin a zaune, ya ƙarƙare wayar ya saka a aljihunsa. "Dama har zuwa yanzu baka taɓa ganinsa ba, baka san kamaninsa ba?" "Eh" ya bata amsa a taƙaice. "Hmm" "Ko zaki bani hoton nasa ne?" "Ni a su wa?" "Ke a 'yar kankamba mana, samunki da hotonsa ai ba abun mamaki bane ba" Nabila ta yi murmushi, kawai ta cigaba da aikin da yake gabanta. **** Mutumin da yake zaune a cikin ofishin sa, ya kalli P.A ɗin Indabo ya ce "Ɗan sake duba na da kyau mana malam" P.A ya ce "Na kalleka" "Shekaru huɗu rak idan Allah ya bani aron rai, suka rage mini nayi retire, a tarihin aikina, ban taɓa karɓar cin hanci na aikata son zuciya ba, ban ƙi ba wasu lokutan ina karɓa in yi abun da ya dace, duk da hakan ma saɓa doka ne. Ba za a haɗa kai da ni ayi rashin albarka ba, a tozarta harkar shari'a ba, idan na ci amana na tsayawa ƙarya a duniya, wa zai tsaya ni a kotun Allah idan zai yi mini hisabi, a cikin kai da uban gidanka, waye zai ƙwace ni? Tambayarka nake yi, na ce waye zai ƙwace ni? Kotun Allah saɓanin tunanin ɗan Adam ce, kuma wallahi dukkanin mu, sai mun tsaya a wannan kotun, kotun da bata buƙatar lauya, ɗan sanda balle ka yi tunanin bayar da cin hanci. Duk da na san badaƙalar da ake tafkawa a cikin harkar shari'a, na yi mamakin wasu abubuwan da yarinyar nan ta din ga faɗa, yar cikina ce amma ina sauraron programs ɗin ta, kuma ko kaɗan ban ji haushin yadda take tsigalewa aikinmu ba, yadda ake amfani da mu, ake aikata abun da ake so. Babu wani rashawa da zaku bani na karɓa, zan yi abun da ya dace ne kawai, idan kuma aka sake zan yi abun da rai zai ɓaci. Kai in taƙaice maka doguwar magana zuwa gajera, daga sama aka yi mini magana a kan lallai nayi abun da ya dace a kan shari'ar nan, ba a buƙatar kuskure a ciki, kuma ko ba haka ba, ni sonake na gama aiki na ajiye shi lafiya" P.A ya jinjina kai ya miƙe tsaye, ya ce "Hakan ma babu laifi, muna godiya sosai" ya juya ya fita daga office ɗin. *** Missed call kusan uku Nabila ta yi wa Viper, amma bai ɗaga ba, sai da ranta ya sosu, ta rasa irin wannan murɗaɗɗen hali nasa, gashi ko zata yi fushi da shi, na ɗan lokaci ne, ana jimawa ta manta. Viper kuma fitowar sa kenan daga wanka, ya kalli wayarsa ya ga missed calls ɗin ta, har guda uku. Bai kula ba, ya fara ƙoƙarin neman kayan da zai saka, wayar Walid ta far ringing. Walid ya ɗaga yayi sallama, ta amsa ta ce "Oga walid barka da wannan lokaci" "Yauwwa barkanmu barrister, ya aiki ya jama'a" "Alhamdilillah, ina ta kiran Viper ya ƙi ɗagawa, wai ni ko wani laifin nayi masa ya tsane har haka ne?" Walid  ya kalli Viper, sannan ya ce "Wanka yake yi yanzu ya fito" Ta ce "Ai dama kai kare shi zaka yi, baka taɓa yadda yayi laifi, ko yayi laifin sai ka kare shi, dama magana nake son mu yi da shi, kuma na ma fasa barshi kawai, sai anjima" Da sauri Walid ya ce "A'a ba za a bari ba, ko na haɗa ki da shi?" "Ba zai kulani ba ai na sani, shiru zai yi mini kamar kurma, in dai yana lafiya shikenan sai anjima" "Kin ga Nabila, tsaya ki ji mana, gaba ɗaya ke ce baki fahimci Al'amin ba, ba wulaƙanta ki yake yi ba" "Ba wulaƙanta ni yake yi ba kace? Idan ba wulaƙanci ba, mai zai sanya ya ce baya so na, wallahi ban taɓa cewa ina son wani ba, ina zaman zamana, ƙaddara da rashin ya ja ni ya kai ni har in da yake, yayi ta wulaƙanta ni bai damu da rayuwata ba, amma ko haushi bana ji naƙi zuciya, ko kwana biyu nayi ban ji ɗuriyarsa ba sai na damu" ta ƙarasa maganar cikin damuwa, da alama abun ya na damunta sosai da sosai. "No, Viper mutumin kirki ne, kuma abun so, in dai ka zauna da shi zaka so shi, saboda yana da halaye masu kyau sosai da sosai, kina kallon muma da muke tare da shi, wasu lokutan haka yake yi mana, amma muna duba halaccinsa a garemu ne, kema baki fahimce shi bane" "Ba wani ban fahimce shi ba, kalli yadda na shiga siraɗin gobarar nan, na zo nayi hatsari, amma sannu kawai ba wani abu ba, ya kasa ce mini" Walid ya ce "Ki yi haƙuri, halinsa ne a haka, amma zan iya ce miki, bayan iyayenki, akwai wanda ya kai shi shiga damuwar abun da ya faru da ke" "A hakan? In kusa rasa raina har karo biyu?" Babu tsammani Viper ya fizge wayar hannun Walid, ya kashe ya dire masa ita, ya fice. Walid ya bishi da kallo yana kallon ikon Allah, shi bai rarrasheta ba, kuma ya hana a rarrasheta. Ko da ya fice daga gidan, wayarsa yake kallo, yana jin tamkar ya kirata, har ya ɗaga ya kalli lambarta, sai kuma ya tsaya ya cigaba da kallon lambar, fasawa yai kawai ya mayar da wayar aljihunsa ya yi gaba. *** "Arfa, wai meyake damunki ne duk kin wani rame kin tsotse" Sumayya ta yi maganar tana ƙare mata kallo. Baba magajiya ta ce "Gara dai ki yi mata, ko ta ji, taƙi gaya mini meyake damunta, sun samu saɓani da babanta, kuma sun shirya, amma kwanan nan sai ƙarewa take yi kamar kuɗin guzuri, ko abincin kirki ba ta ci, duk ta zube sai uban nono da take kayansa kamar ya rinjayeta" Sumayya ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "Wallahi kuwa baba magajiya, da 'yar ƙibarta tafi kyau, haba jarumar mu, idan ki ka saka damuwa a ranki, mu wa zai bamu ƙwarin gwiwar? Muje mu zanta na ji menene ya faru". Suka tafi ɗakin Nabila, Nabila ta zauna a gefen gado, sumayya ma ta zauna ta ce "Gaya mini menene? Naji baba magajiya ta ce kun yi faɗa da Abba, me ki ka yi?" Ta kalli sumayya ta ce "Sumayya haka soyayya take dama?" "Soyayya kuma, ita ta hana ki cin abincin ki ke ramewa?" Ta girgiza kai ta ce "Ba ita ta hana ni cin abinci ba, damuwoyi ne kashi-kashi suka sha mini kai sumayya. Da fari nifa zuciyata na azalzalata a kan son ganin mahaifina, ina son sanin waye shi, ko yaya yake a bani dama na san shi, ni zan fara bincike ta ƙarƙashin ƙasa da kaina" "A'a Nabila, kar Abba ya sani ransa ya ɓaci" "Sumayya ya zan yi, ni ba na son na mutu ban san babana ba, idan a gidan babana nake, wani abun ba za ayi mini shi ba" "Naji, zamu dawo kan wannan batun, naji kina maganar soyayya" Ta numfasa ta ce "Ƙaddara ta kaini ta baro sumayya" Sumayya ta waro ido ta ce "Kamar yaya?" "Son abun da ba zan samu ba nake yi" "A'a kar ki ce haka, amma wa ki ke so ɗin tukuna ma dai" Nabila ta tashi, ta saka key, ta buɗe wardrobe ɗin ta, ta ɗaukko file ta zo ta ajiye a gaban Sumayya. Sumayya ta ɗauka ta fara bubbuɗewa, ta tsaya ta gama dubawa sannan ta kalli Nabila cikin matsananciyar kiɗima da tashin hankali ta ce "Ban gane me ki ke nufi ba haryanzu Nabila" Nabila ta goge hawayen da ya gangaro mata, ta sunkuyar da kanta ƙasa. Ta daki kafaɗar Nabila ta ce "Kin san in da mutumin nan yake, da gaske haɗuwa ku ka cigaba da yi da shi, har ki fara son ɗan daba?" "Ɗaga murya zaki yi, ki tona mini asiri Sumayya" "Nabila wannan hauka ne, ga yaya Nasir a cikin gida, yana ta haƙilo yana fama, ko ɗazu an kawo mana sanarwa, yan sanda na cigaba da nemansa ruwa a jallo, duk wanda ya nuna in da yake, ko in da za a same shi, akwai kyauta, kawai ki ke zuwa in da yake, idan aka kama da ke fa? Menene sunanki bayan mun gama fitowa duniya muna ɓaɓatu da nuna mu masu goyon bayan gaskiya ne?" "Ban damu da abun da duniya za ta ce ba, ko yadda za a kalleni ba, zan tsaya a bayan gaskiya ne duk rintsi duk wahala. Sumayya zan tsayawa Aminu Viper, kuma kamar yadda ki ka faɗa tabbas ina haɗuwa da Viper, kuma na san in da yake, amma ba zan taɓa bari hukuma ta kama shi ba" Sumayya ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wace lalacewar ce ta same ki har haka Nabila? Kina ya mace, ki ke zuwa wurin ɗan daba mashayi, dan ta'adda?" Ta girgiza kai ta ce "Sumayya ƙaddara ce, kamar yadda na gaya miki da farko, idan zaki rufa mini asiri ne shikenan, idan kuma tona mini asiri zaki yi, kina da zaɓin yin wanda ya dace". Ta tashi ta nufi wardrobe ɗin ta, ta mayar da file ɗin. "Kai!! Nabila ki canza tunani, ni ba zan bari ki cutar da kanki, ina kallonki ba" "Ai ba gaya miki na yi, dan ki bani shawara ba, na riga na yanke abun da nake ganin shi ne dai-dai" Sumayya ta ɗauki jakarta ta fice, tana zare idanunta, dan tabattar da ba mafarki take yi ba, dan bata taɓa tsammanin wauta da haukan Nabila ya kai wannan limit ɗin ba. Bayan tafiyarta, Nabila ta duba wayarta, ta ga announcement ɗin jami'an tsaro, ta ɗauki, jakarta ta saka kayanta, ta faki ido ta fice daga gidan. Sumayya kamar za ta yi kuka, ta marairaice a waya ta ce "Sir dan Allah ka yi wani abu a kai, rayuwarta zata shiga cikin hatsari da matsala, za ayi mata kallon mutuniyar banza, ɗan ta'adda take shirin kasadar karewa" Yayi murmushi ya ce "Sumayya ƙawarki ba ta ji, bar ta ai ɗaukaka take nema, mu yi mata fatan nasara" "A'a sir, dan Allah ba zata iya ba" Kankarofi ya ce "Haka ta ce miki? She can do it, ni na bayar da file ɗin sa aka kai mata, ki ja da baya ki tayata da addu'a, in da ki ka ga ana buƙatar taimakona kuma, ki yi mini magana kar ki yi ƙoƙarin dakatar da ita, wannan gargaɗi nake yi miki" ya kashe wayar. Sumayya ta ce 'Naga ta ta kaina ni sumayya" *** Suna zazzaune a ɗakin, suna ta shan sigari, ya ɗaga kai kawai ya ganta a tsaye a ƙofar ɗakin, tana kallonsu, ko sallamarta bai ji ba. Ta rame sosai da sosai, duk da fuskarta kawai ake iya gani, saboda facemask. Ganin ya tsareta da nasa idanun, ya sanya ta sunkuyar da kai, waiwayawa su Walid suka yi, su ga me yake kallo, suka ga Nabila a tsaye. Liti ya ce "Su 'yar anace ce da yamaccin nan ashe" Walid ya ce "Afuwan barrister, kin zo mun cika wurin da hayaƙi, gashi ke ba kya son hayaƙi" Viper ya yinƙura ya tashi, ya ce "Ki tsaya karki shigo, ki zo kina sumewa mutane sai an ta jagwalgwala ki" yayi maganar yana nufota, sai da ya tunkarota sosai, sannan ta lura rigar jikinsa sunansa ne a jiki, an rubuta Viper, da zanen kan macijiya a  jiki ta fito da harshenta. Ya fito ya tsaya, yayi crossing lega ɗin sa, irin ina saurarenki. Banza tayi masa ita ma, suka cigaba da tsayuwa, sai dai tsayuwar bata damunsa, ita kuwa ta fara gajiya, yana zuƙar sigarinsa, yana fesarwa a gefe. Hannunsa ta kalla ta zare sauran sigarin ta yar a ƙasa, ya kalleta amma ta haɗe rai. "Ina jinki ya aka yi?" "Alhaji mu'azzam da ku ka haɗu, dama ka san shi ne?" "Haka ya ce miki?" "A'a, tambayarka kawai nake" "Ki bar maganar sa kawai" "Saboda me?" Ya ce "Saboda haka na ce" "Nifa ina tsoron sai na je gaban kotu, in tarar da wasu abubuwa da ban san da su ba, na rasa yadda zan ɓullowa lamarin, ka gaya mini shi menene alaƙarka da shi?". A hasale ya ce "Na ce ki bar maganarsa ko? Na san shi, amma sanin waye shi ɗin ba shi da wani amfani". "Shhhh ka daina yi mini shouting, ka yi shiru ka saurare ni, aikina nake yi malam" tayi maganar tana kallon ƙwayar idon Viper. Ayshercool 08081012143 72 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 *Ina ma'abota bibiyar litattafan bright pens, ƙarƙashin mikiya writers association, marubutan da suka kawo muku CUTARWA, MUNAFUKIN MIJI, YI WA KAI, A first batch ga second batch, ƘARFE A WUTA, MUTALLAB ya fara zuwar muku da na sa saloz sai kuma ZAYTOON DA HADARIN GABAS NA NAN TAFE SUMA A CIKIN WANNAN WATAN, KAR KU BARI A BAKU LABARI. Waro ido suka yi waje, jin abun da Nabila ta yi wa Viper, liti ya doko tsalle yana faɗin "Ke! Saken da ki ka samu har ya kai haka, mai zamanin ki ke yi wa tsawa?" "Nayi ɗin, kai kuma a suwa?" Tayi maganar cike da son huce takaicinta a kan liti. Walid ya yinƙuro ya fito, amma Viper tuni ya danƙi ƙeyar Nabila, Walid ya yinƙuro, amma Viper ya ɗaga masa hannu, ya yi waje da Nabila. Sai da ya yi nisa da ita, sannan ya saki ƙeyarta, ta ja da baya, tana ƙifta idanu. Ya taka a hankali ya ƙarasa gabanta, ya tsaya ya kalleta ya ce "Ni ki ke wa tsawa a gaban jama'a ko?" Ta sunkuyar da kai, tana yamutsa fuska tare da tura baki. "Karki yi ƙoƙarin tsallake iyaka, ki kaini bango, idan na yi magana bana son jayayya, ki ƙyale wannan maganar, ki tafi da id card ɗinki zan tura miki adress ɗin da zaki je, a asibiti ne kiga shaidan da nake da shi, wato madaki. Ta ɗago ta kalleshi ta ce "Kai ba zaka je ba?" Ya girgiza kai ya ce "Tsoro nake ji, na samu labarin yayanki ya ƙara tsananta nemana kar ya kamani" Nabila ta ce "Hotonka yake nema, ya ce a samo masa hotunanka, ina tunanin hotunanka za ayi sharing ace ana nemanka" Ya ce "Duk neman da yake yi mini ma bai sanni ba, a confused blind man" yayi maganar tare da yin murmushi. Sai da ta kuma kallonsa, ganin yana murmushi, murmushin ma a nutse yake yi. Kallonta da ya yi, ya sanya ta daina kallonsa, ya ce "Amm kwanaki, kamar akwai maganar da ki ke son ki yi mini, something like wani abu yana damunki" "Baka tambaye ni a lokacin ba sai yanzu, ka manta ba wani abu bane, ya wuce" tayi maganar cikin tsiwa, tana kawar da kanta gefe. Kallonta yayi, bai ce uffan ba, ya zira hannu a aljihunsa, ya ciro wayarsa, ya danna ya saka a kunnensa, ya ce "Kawo mini abun nan, na ƙasan katifata, ina wajen bishiyar kalgon nan" Shiru ya wanzu a tsakaninsu, sai ga ɗan mama ya ƙaraso, ya miƙawa Viper envelope, ya saka hannu ya karɓa ya ce "Zaka iya tafiya" Ya kalli Nabila ya ce "Gashi, wani abu ne daga aikinki ne na fara biyanki wani abu, idan komai ya kammala, in sha Allah zan yi miki kyakykyawan biya" Ta karɓi envelope ɗin ta jujjuyata, ta saƙala masa a hannunsa ta ce "Da dan kuɗi zan yi maka aikin nan, da ba zan yi shi ba, bana buƙatar kuɗinka, a wurin Allah nake neman ladan abun da zan yi maka, ba wai dan halinka ba" Shi ma ya jujjuya envelope ɗin, ya ce "Rashin sani, ya fi dare duhu, abun da yake ciki yafi kuɗi muhimmanci a wurinki, zaki dawo ki nema da kanki, shikenan a sauka lafiya" Ta shagwaɓe fuska tana kallonsa, shi ma ita yake kallo, ji yake kamar ya tambayeta me yake damunta, ta rame, amma ya kasa. "Kayi haƙuri" "Da me?" "Kayi haƙuri ka bani" Ya zira aljihunsa ya ce "Ai kuma kin yi wa kanki, maganin mara kunya, wuce ki tafi gida, kan a fara nemanki" Ta sake marairaicewa ta ce "Dan Allah" Viper ya ce "Kar ki ɓata mini rai, wuce ki tafi" "Korata ka ke yi ko? Dan Allah meyasa ka tsane ni ne? Me nayi maka?, Kalli duk rashin lafiyar nan da nayi, ko sannu fa Viper, sannu kawai baka iya yi mini ba, abun yayi mini zafi fa" "Really?" Ta haɗiye wani abu mai ɗaci, ta gyaɗa kai ta ce "Shikenan, bari na tafi, in sha Allah zan yi duk abun da ya dace" ta juya zata tafi ya ce "Amm meye ma sunan naki? Abla ko?" Ta waiwayo ta kalleshi, ta fara tunanin a ina ma aka taɓa kiranta da wannan sunan?. Ta girgiza kai ta ce "A'a Nabila" "Ohh, sunan yayi mini tsayi, just accept it Abla" Kamar ba yanzu ya gama yi mata wulaƙanci ba, ta ce "Nice one, na gode sosai" tayi maganar tana ɗaga masa hannu. *** "Hello, Salim kana ina ne?" "Bokan turai, ya aka yi ne?" "Dan Allah gida nake son ka samo mini" Salim ya ce "Gida kuma?" "Eh salim, amma ba na son kowa ya sani, a wajen gari kuma, saboda na san daddy zai saka a fara bibiyata, sun dage lallai sai sun gano in da rahama take". "To kai yanzu hakan da ka ke yi kana ganin shi ne dai-dai?" Abdul ya ce "Shi ne, dole zan danƙata a wurin iyayenta, na kai ta makaranta kafin su san in da take" "Abdul, ina tsoron abun da zai biyo bayan abun da kake yi ne?" "Salim, rayuwar rahama nake ƙoƙarin karewa da ingantanwa, dan Allah ka taimaka mini, kar a kuma cutar da yarinyar nan a wannan karon" "Shikenan, babu damuwa za a duba in sha Allah" "And sirri ne Please, ko saif ba na son ya sani" "Haba mutumina, ba sai ka jaddada mini ba, you are safe" "Thank you" *** Kankarofi yana zaune a kan gadonsa, yana daddana wayarsa, ya ci karo da lambar Hafsat. Ya yi shiru yana kallon lambar ta ta, ya shafi saman lambar yana tuno ta, yarinyar ta nuna masa so, kuma shi kansa ya san ba dan yana son ta ya aureta ba, amma beside his wealth, ta so shi, ta yi iya ƙoƙarin ta a kansa, amma ya kasa sakewa da ita, yayi mata adalci, har auren ya mutu. Amma ita jidda bai ji haka a kanta ba, hasali ma sosai suke gogawa ita da Safiyya, duk da dama Jidda tsohuwar budurwarsa ce, lokacin tun suna jam'iyya ɗaya da Indabo, kuma za su yi sa'anni da Safiyya, ita kuwa hafsa yarinya ce dama. Ya ji ciwon rashin samun auren jauhar da bai yi ba, amma duk da haka yana yi wa Allah godiya, da ba jauhar ya aura ta wahala suka rabu ba. Shiyasa ko zai ƙarar da duk abun da ya mallaka, sai ya tabattar da indabo ya girbi abun da ya shuka, ba ƙanwarsa yake aure ba, ko babarsa yake aure, bai ji zai iya ɗaga masa ƙafa ba, kisan mummuƙe zai yi masa, kamar yadda shima indabon yake yi. Jidda ta ce ta shigo ɗakin, sanye cikin doguwar riga, ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi, ya ce "Ya dai?" Ta yi guntun tsaki ta ce "Nifa gaskiya na gaji" "Da me?" "Haryanzu ana yi mini sintiri a kan rashin mutuncin da Abdul yayi, yau wannan ya zo, gobe wancan ya zo, duk security ɗin nan, gaskiya ni kawai ka canza mini gida, mu bar estate ɗin nan, na gaji wallahi" "Mu bar estate ɗin nan, amma ɗaya gidan kin san na sister ɗinki ne, a nan suke zama idan sun zo hutu" "So find another one mana, am tired hell of all this, abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, tun da abun ya faru ban sake ganin Abdul ba, ga babarsa ta kira ni tana nema ta gaggaya mini magana, wallahi rashin ramma a gidan nan, gaba ɗaya bana samun komai yadda nake so, khalifa da ansar haryanzu suna tambayata, yaushe yarinyar nan zata dawo, sun saba da ita, Abdul yayi mini hauka wallahi " har ta gama surutanta, murmushi kawai Alhaji mu'azzam yake yi, bai ce mata uffan ba. *** "Hello Ambassador Tahir Arabi" "Distinguish, ya aiki ya Nigeria?" "Alhamdilillah" "Masha Allah, dama maganar yaron nan ne" Indabo ya ce "Na wurina? Jafar?" Amb Tahir ya ce "Eh shi, wallahi distinguish sai haƙuri, sun bawa America shi, kuma yana daf da fara fuskantar shari'a, kuma na lura babu wani abu da embassy ɗin mu zasu iya yi a kai, duk da dai haryanzu muna cigaba da ƙoƙari" Indabo ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Ambassador ba wani abu da za a iya fa ka ce?" "Wallahi kuwa, ka san kisan kai yayi a amurka ya gudu Mexico ya cigaba da harkar ƙwayoyi da hodar iblis tsakanin Nigeria da mexico, yadda aka shirya kama shi, akwai ƙwarewa sosai da sosai, bisa ga wata yarjejeniya da haryanzu bamu san ta mecece ba tsakanin Amurka da mexico suka basu shi, wataƙila musayar fursunoni suka yi" Jiki a sanyaye Indabo ya ce "Na gode sosai da sosai" Ya katse wayar ya dafe goshinsa ya rasa abun da yake yi masa daɗi. ***** Da daddare Nabila na kwance, tana ta tattara bayanai a kan shari'ar Viper, sai ƙarfe ɗaya na dare, sannan ta samu sukunin kwanciya. Ta janyo wayarta, tana duddubawa, ta ga lambar Viper, kawai ta danna kira. Bisa ga mamakinta kawai ta ji ya ɗaga. Ta ce "Viper" "Mmm" "Ba ka yi bacci ba?" "Mmm" Tayi murmushi ta ce "Me ka ke yi ba ka yi bacci ba?" Muryarsa ƙasa-ƙasa kamar mai jin baccin ya ce "Abun da ya hanaki bacci ne hana ni" Ta ce "Wai ni? Ai ni soyayya ce ta hana bacci" tayi maganar tana murmushi. Viper ya ce "Nima haka, tunani da kewar matata ne ya hana ni bacci" "Ai addu'a zaka yi mata" "Ina yi mata, zafi ya dame ni, ina missing fankata" yayi maganar very serious yana lumshe idanunsa. Nabila ta ce "Fanka? Wace irin fanka kuma? Ya ce "Fankar solar ce, iskarta daidai ba mai cutarwa ba" Nabila ta ce "To ko sayo fankar za ayi, ban zaci ana zafi a wurin nan ba ai" "A'a nikaɗai nake jin zafin ai" Tayi dariya ta ce "Ko ƙiba ka yi ne? Zan sayo maka fanka in sha Allah" Viper ya ce "Ki ƙyale maganar fankar nan, ba ki da kuɗin sayenta, ba irin wadda nake buƙata zaki saya ba" yayi maganar yana juyi tare da gyara kwanciyar sa. "Ka gaya mini, zan sai maka in sha Allah, wace iri ka ke so i promise" Ya ce "Ba zaki iya sayenta ba" "Ka gaya mini, zan nemota in sha Allah" Viper ya ce "Ita fankar?" "Eh mana" Kawai ta ji yana dariya, har da gyaran murya. "Kai, dama kana dariya?" Tayi maganar tana tashi zaune. Yayi shiru bai ce komai ba. "Viper" "Mmm" "Dan Allah me ka bani a envelope ka ce zan dawo ina nema da kaina?" "Ki manta, ya wuce kawai, zan baki address ɗin nan, ki je ki samu mutumin nan" Tayi ajiyar zuciya ta ce "To, kayi bacci mai daɗi" "Zafi ya dame ni, ba zan iya bacci ba" Ta ce "Ka tashi liti yayi maka fifita" "Na gaya miki fanka nake so ai, sai da safe" "Ai ka ƙi gaya mini wace iri ce, dan dai fanka sai na saya maka, shikenan yau na ci pass an yi mini dariya" "Hmm" kawai ya ce. Ta sake cewa "Viper" "Kar sunan ya ƙare" Tayi murmushi ta ce "Sunan daɗin faɗa, Viper, in shot kuma V.Snake" ta faɗa tana murmushi. Ta sake cewa "Wai a ina aka yi maka rigar nan, nima ina so" "Wacce?" "Wadda aka rubuta sunanka a jiki" "Nawa zaki saya?" Gyara zama tayi, jin yana kulata yau. "Ayi mata kuɗi, zan saya ko nawa ce, ka san wani abu, idan Allah ya sa muka yi wining a court, rigar nan zan saka in yi ta yawo ina murna" "To, Allah ya bamu sa'a" "Amin V snake" Wasu lokutan simple da shi, wasu lokutan kuwa, sai ka rasa gane kansa gaba ɗaya. Ta ce "Sai da safe" "Hmm" kawai ya ce, ta katse kiran. *** Sanarwa ko ta ina, a kan tsananta neman Al'amin Viper, tare da alƙawarin kyauta mai tsoka ga duk wanda ya nuna ko ya bayar da information a kan in da za a same shi. Nabila ta damu sosai, ga Sumayya ta daina ɗaga wayarta, dan haka ta shirya tsaf, ta tafi wurin aikin sumayya. Sumayya na ganinta ta haɗe rai, Nabila ba ta yi fushi ba ta ƙarasa in da take ta ce "Sumayya ba kya ɗaga wayata meyasa?" "Ban sani ba, na gaji da wahalar da ki ke saka mu ne, babu dalili Nabila, daga wannan sai wancan? Gaba ɗaya kin hanamu nutsuwa da sukuni, ki jijjigo mana wannan masifa muna zaune, wane irin kallo ki ke so ayi miki, idan aka ga kin koma bawa ɗan ta'adda kariya, hukumar yan sanda na nemansa ruwa a jallo, ke kina tare da shi" "Sumayya, baki yi mamakin yadda na sauya lokaci guda ba? Har kin manta huci da haƙilon da nake yi a kan a kama shi, kwatsam ki ji na koma na ce zan tsaya masa na bashi kariya, ayar tambaya yakamata ki fara saka mini, meyafaru?" Sumayya ta ce "Ba wani in tambayi meyafaru, kawai ki cire kanki daga wannan sabgar" Nabila ta ce "Wallahi ba zan ajiye ba, ko me za ayi mini" kawai ta saki baki tana kallon Nabila. "Ko dai ki tayani a wannan karon ma, ko kuma ki ƙyale ni ki zuba mini ido, yanzu ya maganar program" Sumayya ta ce "Mhmm yana nan, Nabila ni yanzu kin daina bani mamaki tsoro ki ke bani, yanzu duk bala'in nan, kin san in da Viper yake" "Ƙwarai ki gaya wa uban kowa da ki ke so masoyiyya" "To, Allah ya taimaka" "Amin, gama mu tafi ki rakani wani wuri" Sumayya ta ce "A'a ba zaki kai ni in da za a kashe ni ba" Nabila ta ce "Wane irin kashe ki kuma, mu je dan Allah" "To ki tsaya na kammala abun da nake yi, sai mu tafi" Ta kammala abun da take yi, suka fita,  tare da sumayya. Tiryan-tiryan suna tafe, har ƙofar ɗakin da Viper ya rubuto mata, wasu masu sanye da kaki, suka tarar a ƙofar ɗakin a tsaye, Nabila suka gaisa, ta ciro id card ta nuna musu. Suka ce ta shiga, amma ban da sumayya, Nabila ta ce "Ita ma ma'aikaciya ce, yar jarida ce" Suka ce "A'a kekaɗai aka ce mu bari ki shiga". Sumayya ta ce "Ba damuwa, zan jira ki a nan" Nabila ta shiga, ta yi sallama ta tarar da mutum a zaune a kan gado, hannunsa ɗaya an saka masa sarƙa, ƙafarsa kuma ɗaya an yanke ta. Ta ƙarasa gaban gadon, ta ja kujera ta zauna, ta kalleshi ta ce "Sannu malam" Ya ce "Yauwwa" Ta ciro id card ta nuna masa ta ce "Sunana barrister Nabila, na zo ne a kan case ɗinka da Al'amin mai zamani. Ya ɗago ya kalli Nabila amma bai yi magana ba. "Ka yi magana, dan ka sauƙaƙa wa shari'a, me ka sani game da kisan da aka yi wa matar mai zamani?"ya yi shiru ya ƙi magana. Tayi tayi, amma yaƙi cewa komai, ƙarshe haka ta fito bai yi magana ba. Sumayya suna ta hira da security ɗin wurin, Nabila ta fito, tana ganin Nabila ta tashi ta ce "Kin gama?" Nabila ta ce "Eh mu tafi" Suna tafe ta kira Viper a waya, ta ce "Hello V snake" "Barrister" "Naje wurin gayen nan, amma yaƙi magana, nayi nayi, yaƙi magana" Viper ya ce "Rabu da shi, zai yi ta ƙarfin tsiya, ki tafi kawai" "Ok, na ma taho, amma yakamata yayi magana gaskiya, bari na ƙarasa gida sai anjima" ta kashe wayar. Sumayya ta ce "Nabila wai wurin wa ki ka zo ne?" "Zan yi miki bayani, amma ba yanzu ba" Ta ce "Ok shikenan" *** "Rahama kina ji na?" "Ina jinka" "Zamu sake barin gidan nan" "Zuwa ka mayar da ni gida?" "Wai na mayar da ke gida ki yi me? Ai kin san iya wuya muna tare, nan zamu bari temporarily, daga can kuma zan kai ki gida, sai kuma makaranta, a abuja zaki koma da karatu ai" "Yar ƙauye a Abuja, to ai ban iya turanci ba, ni gaskiya na fi son makarantar garinmu" Abdul ya yi dariya ya ce "Ai Shiyasa zaki je Abujan, zaki iya turanci, kan ki gama ki ƙara gogewa ki zama her excellency rahama" "Taɓ abun ma ba tsari" "Kamar ya babu tsari?" "Wata zaka aura ai, kuma ni a lokacin mutane zasu ji daɗin nuna ni suna aibata ni" Abdul ya girgiza kai ya ce "Muna tare, babu wanda zai aibata mini ke" Ramma ta yi murmushi ta ce "Ba zaka iya canza komai ba, ɗabi'ace ta al'ummar hausawa" Ya ce "Shikenan, mu bar maganar" Ta ce "Ya dai fi" Wayarsa ya ɗaga, ya ɗan gyara zamansa ya ce "Na'am Mummy" "Wato Abdul kafi son ka yi ta sakani a tashin hankali da damuwa ko?" "Mummy me nayi kuma?" "Ban sani ba, ka saka babanka yana yi mini kallon ni nake goya maka baya ka ke yi masa rashin ɗa'a, ka fito da yarinyar nan ka huta su huta ka ƙi, rashin mutuncinka har ya kai ka ajiye mace kana lalata da ita, bayan na keta mata haddi,, ga ɗan uwanka can an mayar da shi america, sai abun da Allah ya yi, shiyasa ake ta fafutukar ka zama gwamnan nan ko a samu ya fito, amma ka ƙi, ya ka ke so na yi Abdul, in bar muku duniyar ka huta ko?" Cikin damuwa ya ce "Mummy ki yi haƙuri dan Allah, ki fahimce ni, ya za ayi na so ki mutu, ba haka bane ba. Wallahi Mumm tsoro nake ji na fito da yarinyar nan, ayi mata wani abu na daban, dan Allah ki yi haƙuri, zan zo gida nayi miki bayani, na san zaki fahimce ni in sha Allah. Kuma yaya jafar zai fito in sha Allah, ki yi haƙuri dan Allah" "Ai shikenan, ka yi abun da ka ke so" "A'a ba za ayi haka ba, zan zo har gida nayi miki bayani" ta katse wayar, yayi ajiyar zuciya yana lumshe idanunsa ya buɗe yana kallon ramma, da ta yi kamar ba ta jin me yake faɗa a wayar. "Rahama" "Na'am" "An sakoni a gaba a kanki" "An san ka sace ni kenan?" Abdul ya ce "Ke fa ba a abun arziki da ke, ke da ban sace kin ba, da yanzu wani zancen ake ba wannan ba" "Ai ba da kyakywar manufa ka sace ni ba, kashe ni ka ce zaka yi" "Amma ai ban kashe kin ba ko?" Tayi masa shiru ta cigaba da aikin ta. **** Nabila ta fito daga banɗaki, kawai ta tarar da Nasir a tsaye a ɗakinta, ta kalleshi ta ce "Lafiya?" Ya ɗago mata file ɗin Viper da yake hannunsa, ta bar shi a kan gadonta tana aiki, ya faɗo mata ɗaki. "Menene wannan?" Ta ƙarasa gabansa ta saka hannu zata karɓa, ya janye yana sake tambayarta "Menene wannan Nabila?" "Babu ruwanka da ko menene, ka bani file ɗina kuma ka daina shigo mini ɗaki ba tare da iznina ba" Cikin tsawa ya ce "Ki yi mini bayani kin tsaya kina wasu kame-kame da wasu maganganun banza da na wofi" Cikin dakewa ta ce "DSP aikina nake yi, ka fita daga harkata ka bani file ɗina" "Nabila, ta tabatta goyon bayan ɗan ta'adda ki ke yi?" "Ni bayan gaskiya nake bi, kawai, ka bani file ɗina" "Nabila kina haɗuwa da mutumin nan, kin san in da yake" "Ni ban san in da yake ba, ka bani file ɗina tun ina ganin mutuncinka" Shammatarsa tayi, ta kafa masa haƙora a hannunsa, ba shiri ya sakar mata file ɗin, ta kwashe abun ta tayi waje, ya bi ta da kallo, ya kalli hannunsa yadda yake tsatstsafar da jini saboda iya ƙarfinta ta cije shi. Cikin yarfe hannu, ya bi bayanta, sai dai ko sama ko ƙasa ya nemeta ya rasa a cikin gidan nan. Zuciyar sa ta daɗe tana mamakin abun da ya gani, amma haryanzu ya kasa gazgata cewar Nabila tana haɗuwa da Viper, ta san in da yake, amma me zai haɗata da ƙasurgumin ɗan ta'adda haka tana ya mace, idan kuwa haka ne, duk hukuncin da doka tayi a kanta shi ba zai ce komai ba, amma ya yanke ya sake tuntuɓar Abba, ya kirata ya ja mata kunne, a lallaɓata a cikin gida idan da abun da ta sani, a sasanta abun, kar asiri ya tonu, dan shi kansa abun kunya ne a gare shi, ace yana can yana haƙilon neman ɗan daba, Nabila na zagewa ta haɗu da shi a ɓoye. Da daddare Nabila na zaune a falon Abba, ga Nasir a gefe, sai kuma shi kansa Abban, tayi shiru ta sunkuyar da kai fuskarta babu annuri. "Arfa" Abba ya kira sunanta a kausashe. "Na'am Abba" "Gaske ne abun da ɗan uwanki ya gaya mini?" "Abba ai ban san me ya gaya makan ba" Abba ya gyara zama ya ce "Gaske ne, kin san in da wanda yake ta haƙilon nema yake? Nabila meye haɗinki da ɗan daba ne? Kina 'ya mace?" Ta girgiza kai ta ce "Abba ya za ayi na haɗu da wanda yan sanda ma suka kasa kamawa, file ɗin shari'arsa kawai ya gani a ɗakina, kuma ba nawa bane ba, na barrister Habib ne, nima karɓa nayi na duba, ina dudduba yadda aka gudanar da shari'ar sa a wancan lokacin ne, an ce yayi shekara biyar a prison ba ayi masa shari'a, kwatsam kuma aka ce an sake shi, aka dawo ana nemansa sai nake jin kamar akwai wani ɓoyayyen lamari, shi ne nake ta bibiya, ka san muna program da sumayya, so ina binciken cases makamantan nasa shi ne kawai, amma sai zargina yake yi, ni ban san meyasa ba" Abba ya yi ajiyar zuciya ya ce "To kai ka ji abun da ta ce, me zaka ce?" Sam Nasir bai ji ya yarda da abun da Nabilan ta faɗa ba, amma ya ce "Shikenan Abba, tun da haka ta ce" "Dan Allah ku daina wannan rigingimun, da ba haka kuke ba, naga tare kuke sharing working experience ɗinku, amma yanzu kuna nema ku lalata tsakaninku, ni ban ji dama arfa zata iya bin wani ɗan daba ba, tana ƙyamar irin wannan laifukan, dan haka dan Allah duk ku yi haƙuri Allah ya yi muku jagora, ya rufa muku asiri" Nabila ce ta fara miƙewa ta amsa da Amin, ta fice tana hararar Nasir, shi kuma ya bi bayanta da kallo, sam bai yarda da ita ba. Washegari aka dawo da motar Nabila, an gyarota fes har fenti an canza mata, ta ji daɗin dawowar motar nan, dama yawan zirga-zirgar nan ya isheta. Ɓangaren sumayya ma, nata program ɗin da take gabatarwa a kan shirin siyasa, na an yi walƙiyya, yana ta jan dubban masu sauraro, sakamakon yadda take baje wa mutane komai, game da irin kuɗaɗen da gwamantin tarayya take bayarwa domin ayyukan raya ƙasa, ta kan ɗauki ƙananan hukumomin shiyya ɗaya, ta kawo kuɗin da suka samu na wata, na tarayya, na jiha da na ƙanan hukumomin, da iya ayyukan da aka yi musu. Sai dai tun da ta zo kan na Indabo, a ƙalla tafi sati uku, program ɗin a kansa yake, dan sai da ta faro tun daga farkon tenure sa, yadda take hawa da sauka a kansa, zai tabattar maka akwai wata a ƙasa tsakaninta da shi. Yan siyasa da dama, sun kawo wa program ɗin hari, da neman a dakatar da shi, amma hukumar gudanarwa ta tashar suka tabattar da cewa an riga an biya su ɗaukar nauyin program ɗin, dan haka ba zasu dakatar ba, wanda bai gamsu ba, ko ya ji an yi masa sharri ko cin zarafin sa, to ya kai kotu. Da safe Nabila ta fito da motarta, sai ƙyalli take yi, ta batta a kunne, ta shiga gida ta haɗo kayan breakfast ɗin ta, ta koma cikin mota, Viper ya kirata a waya. Ta ɗaga ta ce "Hello V snake" Cikin dakakkiyar muryarsa ya ce "Kin fita aiki ne?" "Ina ƙofar gida ne, yanzu zan tafi ka tayani da addu'a, yau zan kai kokenmi kotu" Ya ɗan ja numfashi ya ce "Ki bi ta farkon layinku, wurin incomplete building ɗin nan, ina nan ina jiran ki" "Ok sir, gani nan" Ta ja motar ta ƙarasa in da ya ce mata, a wurin ta tarar da shi, ya tako a hankali, cikin nutsuwa. Ta zura masa ido tana murmushi ba tare da ta san tana yi ba. Ya shigo ya rufe ƙofar, ta kalleshi ta ce "Good morning" "Morning" ya amsa ba tare da ya kalleta ba, ya ajiye mata baƙar leda. Ta ɗauka ta ciro abun ciki, baƙar riga ce, da sunansa a jiki Viper, da hoton maciji. "Wow masha Allah, har an yi mini? Na gode sosai, wai waye yake yi maka rigunan nan?" Yayi shiru bai amsa mata ba. Sai kuma ta ce "Sanyin Ac yayi maka normal ko na rage?" Kawai ya jingina da seat ɗin motar ya zuba mata ido. Sai ta ɗan rikice ta ce "Menene? Ko wani abun ne?" Still bai yi magana ba. Ji tayi tsigar jikinta na tashi, ta ce "Dan Allah ka gaya mini menene?" "Ina jin ƙwarin gwiwa a kan shari'ar nan, wanda ke ki ka bani shi, and at the same time scared, idan rayuwarki ta salwanta saboda ni, ba zan yafe wa kaina ba, dan rayuwar ki kika saka a haɗari saboda ni, na zo ne in ce miki good luck" Duk da ta takura da kallon da yake yi mata, tamkar ta nutse, ga wata fargaba da bata san ta mecece ba, amma ta dake ta ce "Allah yana tare da mu, in sha Allah zamu yi nasara" "Allah ya sa, ko mun yi nasara ko bamu yi ba, ina da kyakykyawan tukuici gareki" "Ni zuciyarka kawai nake so, shi ne tukuicin da nake so" haɗe rai yayi ya ce "You are not serious, ba zaki daina wannan shirmen ba ko? Wahala zaki yi ta sha kuwa, ba na kallon kowace mace mace idan ba jauhar ba, ki je ki samu wani ku daidaita" yayi maganar ba tare da ya kalleta ba, yana ƙoƙarin buɗe ƙofa ya fita, jikinta har yayi sanyi, idonta ya cika da hawaye" yayi saurin ficewa, ba tare da ya sake kallonta ba. A guje ta fizgi motar, ta bar wurin, wanda hakan sai da ya bashi dariya, dan ya san fushi ta yi. Nabila tana tafe hawaye na zuba daga idanunta, duk ta ɓata kwalliyar ta, sai taga kamar zata yi nasara, kawai sai ya buntsure, gashi ita kullum ƙara son sa take yi so mai zafin gaske. Da haka ta ƙarasa court, ta tsaya ta ƙara gyara fuskarta, sannan ta fita ta shiga cikin court ɗin. Nabila ta nemi kotu, ta hana hukumar 'yan sanda kama Muhammad Al'amin Ibrahim, da aka fi sani da Viper, har sai an yi cikakken bincike a kan kisan kan da aka yi wa matarsa shekaru biyar da suka gabata, hakazalika yana neman hakkinsa, na tsare shi shekaru biyar ba tare da yi masa shari'a ba, a kan laifin da ba shi ya aikata ba. Ta gabatarwa kotu kwafin shari'ar da aka yi masa a baya. Duk da ba ma a fara shari'ar ba, amma haka nan ta din ga jin tamkar ta kama hanyar sauke gingimemen nauyin da yake kanta. Abun da Nabila bata sani ba shi ne, tuni aka kira Nasir, aka sanar masa da an ganta da wani, a wurin sabbin gine-gine da ake yi a unguwar, kamar yadda ya saka CID ta ko ina a kanta. Ya shiga kitchen ɗaukar lemo a fridge ya tarar da wayar Nabila a kitchen tana ringing, ita kuma bata kitchen ɗin, ya ƙarasa in da wayar take, kiran ya yanke. Ya kalli wallpaper ɗin ta Hoton sunan Viper ne, da maciji a kan wallpaper da wani heart. Ya saka hannu ya ɗauki wayar, wani kiran ya kuma shigowa. Kawai ya ɗaga kiran ya saka a kunnensa ya ce "Waye?" "Viper ne, mai zamani Ayshercool 08081012143 73 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Ina ma'abota bibiyar litattafan bright pens, ƙarƙashin mikiya writers association, marubutan da suka kawo muku CUTARWA, MUNAFUKIN MIJI, YI WA KAI, A first batch ga second batch, ƘARFE A WUTA, MUTALLAB ya fara zuwar muku da na sa saloz sai kuma ZAYTOON DA HADARIN GABAS NA NAN TAFE SUMA A CIKIN WANNAN WATAN, KAR KU BARI A BAKU LABARI. Cak Nasir ya ƙame, a daidai lokacin da Nabila ta dawo kitchen ɗin. "Wa ka ce?" "Sarai ka ji abun da na ce, kar na sake kiran waya, ka ɗaga mini, ka bawa mai wayar, zan yi magana da lawyer ta" Hakan yayi daidai da shigowar Nabila da take tsaye a bayansa, ya waiwayo ya kalleta, ya miƙa mata wayar yana tsareta da idanunsa da ya zazzaro su, tamkar zasu faɗo ƙasa. Ta saka hannu ta karɓi wayar, tayi ƙasa da murya, ta ce "V ka kashe ni" "Shhh ki tsaya ki saurare ni" Ta ce "Tom" "Yaya zaki yi da batun shaidun nan? kin ce gayen nan yaƙi magana, ina so zan je in da yake da kaina" "To ai ka ga ni ban san me ma zan ce ba, ban san wace hukumar ta ce ta kama shi ba, dole yan sanda zamu shigarwa koken su kama shi". "Na fahimta, na san abun da zan yi, dama na zata zai yi magana ne, ki samu wani abun as shaida, amma na san abun da zan yi masa, zai yi magana ta ƙarfin tsiya. And am sorry for what i did, na san zan saka ki a matsala, amma hakan ka iya zama maganin wasu matsalolin naki, dole za a zo wurin nan, cigaba da ɓoye-ɓoye ba zai haifar da ɗa mai ido ba, no matter what it takes, duk tsanani da ƙalubalen da zaki fuskanta ki jure, da Allah na dogara, amma kekaɗai ce ƙwarin gwiwa ta, Please don't give up" "Kar ka damu, in sha Allah I won't, i promise you that" "Thank you" ya katse wayar, hankali kwance ta kammala wayar, Nasir ya zuba mata ido, yana jiran ta gama, ya ji wace ƙaryar za ta yi masa, kawai ya ga ta basar, ta cigaba da abun da yake gabanta. Da ƙarfin tsiya, ya janyo kafaɗarta ya tsayar da ita tana fuskantar sa, ya ɗaga hannu zai kwaɗa mata mari ya ji muryar Baba magajiya "A'aaa lalalalaaaaa me zan gani haka, a kul ɗin ka, kar ka kuskura fara me yayi zafi zaka dakar mini 'ya Nasir" tayi maganar tana nuna shi da yatsa, Nabila kuwa da gudu ta gudu ta ɓuya a bayanta, tana ƙifta idanuwa. "Ammm baba magajiya, ki fita daga cikin maganar nan" "Ban gane in fita daga maganar nan ba, zaka kassara mini ƴa ka ɗaga hannu zaka daketa, ƙarfin ka da nata ɗaya ne?" Ai tana rufe baki, ya ture baba magajiya ya danƙo Nabila ya fara janta. Tirjewa ta din ga yi, tana zunduma ihu, tana a taimaketa zai kasheta. Baba magajiya ta sake biyo su, tana yi masa masifar ya saki Nabila. Sai da ya kaita tsakiyar falo, sannan ya kalleta cikin ƙunar rai ya ce "Nabila umarni nake baki, a yanzu yanzu cikin gaggawa ki sanar mini ina wannan ɗan iskan ɗan daban yake, kafin na tafi da ke na kulle ki, Nabila wace irin mahaukaciya ce, kina iƙirarin ke mai gaskiya ce, amma kina take doka kina ɓoye mai laifi?". "Ni ban taka kowace irin doka ba, bisa doron doka nake gudanar da aikina" "Shut up, ki gaya mini in da yake, kafin na saka ankwa ke na tafi da ke, na je na kulle ki" Nabila ta ce "Ka kulleni a nayi maka laifin me?" "Tambayata ki ke sake yi saboda kin raina mini hankali, ko bayan wannan hujjar wata ki ke nema? Am disappointed on you, kin bani kunya Nabila, ban taɓa tunanin duk wannan haƙilon da ki ke yi, zaki iya cin amanar ƙasa ba, kuma ki ci amanata ba" "Ban ci amanar kowa ba, ni ba maciyiya amana ba ce ba" "Ba zaki yi mini shiru ba, sai na tattakaki tukuna? Ki na ɗiya mace daga gidan daraja da mutunci, amma ki zubar wa da kanki kima, dan ba zan ce mu ki ka zubar wa ba, ki gaya mini ina ce maɓoyarsa, kafin ke nayi arresting ɗinki" "Kayi arresting ɗina like how, DSP lawyer ce fa ni, lawyer ma mai zaman kanta, ina da ikon kare duk wanda ya zo gabana ya nemi hakan, duk girman laifin da ya aikata kuwa, balle wannan da makauniyar shari'a kawai ake yi. Ba ka da ikon kama ni, dan ban aikata laifin komai ba" Tuni yan gidan suka tattaru a falo, domin jin meyake faruwa, suke ta wannan uwar hayaniya da yammacin Allah. Sai dai jin turka-turkar da ake yi, ya sanya su mamaki ba kaɗan ba, jin abun da Nabila ta aikata, gaba ɗaya sai suka haɗe mata kai, suka din ga jifanta da miyagun maganganu, na cin zarafi. Mama ta kada baki ta ce "Ai na san a rina, an saci zanin mahaukaciya, ba dai major ya ɗaukaketa ya nuna ita ce ya a gidan nan ba, an zo dai-dai in da nake son a zo, ɗan sa da ya haifa bai ja masa abun kunya ba, wata a banza gashi ta jawo masa, Allah ya sa ba yawon ta zubar take yi ba da sunan aiki, ban da haka, ya za ayi ta din ga hulɗa da ɗan iskan gari da ake nema ruwa a jallo, ta ce shi zata kare mutumin da yayi kisan kai ɗan ta'adda". "Allah ba zai nuna mini yawon ta zubar a rayuwata ba, da ni da 'ya'yan gidan nan, in Allah ya yadda, babu wanda zai yi yawon ta zubar" "Maman ki ke gaya wa haka Nabila?" Yayi maganar yana nuna ta da yatsansa. Ko a jikinta ta ce "Zata iya kallon sauda, ko su siyama, ta ce suna yawon ta zubar? Ko yi suke na san ɓoyewa zata yi ba zata faɗa ba, sai ni 'yar Allah ba ni da ba ita ta haife ni ba, ai na daɗe ina yi mata kawaici kai ma ka sani" Baba magaji sai haƙuri take bayarwa, Nabila kuwa bakinta yaƙi mutuwa, da sun faɗa take mayar musu, mama ta ce wa Nasir, ya rabu da ita ya jira major ya dawo, ya ɗauki duk matakin da yakamata a kanta, kar ya matsa tayi masa wani Sharrin amma duk abun da yakamata ayi mata na doka, a ɗauki mataki a kanta. *** "Abdul, so kake sai baƙin ciki ya kashe ni, ya kashe mahaifinka, mu bar maka duniyar ka rayu kai kaɗai ko? Tun da aka ce masa an mayar da jafar amurka, hankalinsa yaƙi kwanciya, wataƙila hukuncin kisa ne a kansa, jininsa yayi mummunan hawa, an bashi hutu ma zaman majalisar nema yake ya gagare shi, kai ana ta fama ka samu ka zama deputy governor ɗin nan, yanzu ko maganar bikinka ka daina yi, yau an ƙara watanni uku a kan lokacin bikin, amma ko ka bibiya meyafaru ya ake ciki? Babu ruwanka saboda ka ajiye yar mutane kana lalata da ita, so kake sai asirinka ya tonu mu shiga uku baki ɗaya, da wanne ka ke son mu ji? Wancan case ɗin ko kuma naka da ake ta bibiyarka ana lallaɓaka ka ke rashin mutunci?" Ya girgiza kai ya ce "Mummy, ba haka bane ba, wallahi tsoro nake ji na fito da rahama, na san babu lallai abun ya tsaya a iya bayar da shaida a kotu, ina tsoron daddy ya yi mata wani abun, kin san halin sa, idan kuwa aka kuma cutar da ita, ba zan iya yafewa kaina ba, saboda nayi nadamar abun da na aikata" "Ka yi nadama amma ka ajiye musu yarinya, ka ke lalata da ita? Wace irin nadama ce haka?" Ya ɓata fuska ya ce "Ni ajiyeta kawai nayi, ba lalata nake da ita ba" "To yanzu dai na ji, amma tana ina? Ni ka gaya mini, nayi maka alƙawarin babu wanda zai cutar da ita, har mahaifin naka ma, ba zan bari ya cutar da ita ba" Ya ce "Gaskiya Mummy na san lallaɓa ni ki ke yi, kiyi mini wayo, amma na san tsaf zaki bayar da ita" Ta ce "Laaa ƙarya nake yi maka kenan Abdul?" Ya girgiza kai ya ce 'To, zan dai dawo in gaya miki, amma ba yau ba, bari na tafi Asibiti zan je"ya tashi ya ɗauki jakarsa. "Ba zaka je ka duba mahaifin naka ba?" Abdul ya ce "Zan je, yanzu na kusa makara ne, kuma ina zuwa zai yi mini zancen yarinyar nan, sai na dawo tukuna" ya fice daga ɗakin. *** Viper ya ƙurawa madaki ido, da duk yayi wani iri, babu wannan kwarjinin da ban tsoron da yake da shi, babu shaye-shayen ƙwayoyin da ya saba, gaba ɗaya sai tsufansa ya fito sosai da sosai. "Madaki, yanzu na tabatta har labarin madaki ya shafe, Viper ba zai bar zuciyarka ba, ko dan wannan ƙafar da aka yanke, kodayeke taimakonka nayi, ni na fika imani, ba dan haka ba, wannan ƙafar cin jikinka zata cigaba da yi. Na turo lawyer ta, ku yi magana, amma ka ƙi, ni ba ta taka nake yi ba, kai ka san kasheka ba wahala zai bani ba, da kai da muƙarabbanka, amma ba ta kai nake yi ba, zan yi amfani da kai ne, na dangana da Indabo, dan haka ka shirya yin magana ko baka shirya ba?" "Ban shirya ba, kuma ba zan shirya ba, kayi kaɗan mai zamani, haryanzu ba ka kai in da zaka ga bayana ba, maƙiyina bai isa ya ga bayana ba" Viper ya ce "Baya kuwa na riga na ganshi, tun da da hatimin sunana zaka mutu a gadon bayanka, na san duk abun da zan yi maka, ba zan huce ba madaki, ni zuciyata ka yi wa illa, amma zan iya kamantawa. Kar ka manta lakwari ma yana hannuna, sannan shi ya ji wuyar da ya shirya yin magana, dan haka ko ka yi magana, ko kar ka yi tare zata kwaɓe muku, idan yayi tamkar ka yi ne" Ya ciro wani jan gari, mai fatsi-fatsi a cikin yar leda, ya ɗago wa madaki shi, ya ce "Da irin wannan, ku ka yi amfani wurin hanani kataɓus, ku ka yi mini illa ko?" Madaki yayi shiru, yana bin hannun Viper da kallo. "Bari na yi maka amfani da ita, na ga wani irin hali na shiga kuma wane irin nishaɗi ka ji, lokacin da kake cin zarafina" Viper ya miƙe tsaye, Madaki ya zazzaro ido, amma Viper haka ya sheƙawa madaki garin nan. A take kansa ya fara juyawa, ya shiga girgiza kansa. Viper ya ce "Ina son ku ɗauke shi, ku kai shi kusa da tsohuwar dabata, in da yaran nan da yake cin zarafi yake yi wa kisan gilla, wanda ya sanya tsananin tsoronsa a zukatansu, idan dare yayi ku yasar da shi a can, gari ya waye su ganshi a wurin, da ƙafa ɗaya su tabattar da cewa alkadarin sa ya karye, ƙaryarsa ta ƙare. *** Nabila na kwance, ƙirjinta na ta bugawa, jiran dawowar Abba kawai take yi, ba ta san me Nasir zai gaya masa ba, ba ta san a yaya zai karɓi maganar ba. Tana ta maimaita "la haula wala ƙuwwata illa billah" bacci ne ya fara fizgarta, ta ji tsayuwar motar Abba, wajen ƙarfe goma na dare, zumbur ta tashi ta tsaya, ta tafi window tana leƙe-leƙe, har wurin goma na dare, shiru ba ta ji an kira ta ba. Ta ɗauki wayarta, ta kira Viper, bugu ɗaya ya ɗaga, ya ce "Ya ake ciki?" "V am scared" tayi maganar tana fitar da numfashi cike da tsoro. "Meye yake baki tsoron?" "Ban san me Abba zai ce mini ba, tsoro nake ji, Abba bai iya fushi ba, bana tunanin zai fahimce ni cikin sauƙi, na shiga uku" tayi maganar tana fashe masa da kuka. "Shhhhh, Abla" ta ji kiran sunan har tsakiyar zuciyarta. "Mmm" "Shi ramin ƙarya ƙurarrre ne, duk yadda ki ka kai ga ɓoyewa, dole sai ya fasu wataran, shiyasa na kawo ƙarshen zargin da yayanki yake yi miki. Haɗuwar da muka yi da ke, sai da aka gaya masa, yana bibiyarki ko ta ina tasa mafitar kawai yake nema. Ki nutsu ki cigaba da addu'a, babu abun da zai faru in sha Allah, you are my only hope as i told you before, idan ki ka karaya ni ya zan yi?" Yayi maganar cikin rarrashin da bata taɓa tunanin ya iya ba. "Ba zaka gane ba, amma zan cigaba da addu'a, sai da safe" ta kashe wayar tana dafe ƙirjinta, saboda yadda yake bugawa. *** P.A ne ya shiga bedroom ɗin Indabo, bakinsa ɗake da sallama, ya amsa masa ya ƙarasa ya zauna, ya ce "Barka da wannan lokaci" "Barkanka dai P.A" "Ya ƙarfin jiki kuma?" "Jiki Alhamdilillah, da sauƙi sosai, maybe gobe in Allah ya kaimu zan shiga Abuja" P.A ya ce "Yakamata ka ɗan dakata da shiga Abujan nan?" Ya kalli P.A ya ce "Saboda me? Hutuna ya ƙare ai" "Ƙishin-ƙishin na ji, maganar kuɗin scholarship ɗin da na harkar sadarwa, balli na daf da tashi, EFCC zata bincike ku" zumbur indabo ya tashi zaune ya ce "Kai a ina ka ji?" P.A ya ce "Majiya mai ƙarfi, amma ka kira shugaban marasa rinjaye, a wurin P.A ɗin sa na ji maganar, kuma ba jita-jita bane ba" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, P.A wai ya aka yi abubuwa suke ta taɓarɓarewa ne haka?" P.A ya ce "Nima abun ya fara bani tsoro, amma ka dudduba ka bincika mu ji" "Ai ni har bana son kiran waya, duk wanda na kira akwai kalar masifar da zai gaya mini. Kuɗin nan fiye da rabi duk a kan ƙoƙarin ganin jafar ya fito ne, idan ba hali sai na lallaɓa na mayar, amma zan yi magana da ministan sadarwar da na ilimin, mu tattauna, koma dai na saka su bincika mana". "Bayan nan, mutane fa suna ta surut a kan program ɗin da yarinyar nan take yi, na walƙiyya wallahi mutane sun fara dawowa daga rakiyarmu, na rasa uban da yake ba ta wasu information ɗin da take faɗa a kanmu" "Kaga P.A, dan Allah ka ƙyale ni haka, gaba ɗaya maganganunka ba alheri yau, tashi ka tafi dan Allah" P.A ya ɗan yi shiru, sannan ya tashi ya fita. *** Yanayin da Abba ya fito falo, ya tabattar musu da ba lau ba, fuskar nan a murtuke babu annuri. Ya kalli baba magajiya ya ce "Kira wo mini Nabila" sai da suka kalli Abba, jin ya ambaci Nabila, maimakon Arfa da ya saba kiranta. Nabila na kwance baba magajiya ta shigo ta sameta, ta ce "Arfa, babanki yana kiran ki" sai da ƙirjinta ya buga da ƙarfi, ta yi ajiyar zuciya ta ce "To, gani nan zuwa" baba magajiya ta fita daga ɗakin. Da ƙyar Nabila ta tashi, ta nufi falon, ƙirjinta na ta bugawa da sauri. Kusan kowa ya hallara a falon, ita kawai ake jira. Ta ƙarasa ta durƙusa a gaban Abba, ta ce "Abba gani" Mama ta ce "Munafuka ga ladabin kura" Umma ta ce "Ki yi shiru, karya haɗa da ke". "Dama irin tarbiyyar da na baki kenan? Ki je ki dinga bibiyar 'yan iska a waje?" Gabanta ya faɗi, ta ɗaga kai ta kalli Nasir ta koma ta sunkuyar da kai. "Har muka yi zaman kudancin Najeriya, muka gama ki ka yi jami'a, duk baki lalace ba sai yanzu? Ina ke ina bibiyar ɗan daba, ɗan ta'adda kuma ɗan iska da hukuma take nema? Kin zama 'yar iska lalacewa ki ke so ki yi ko, ko ma in ce ki ka yi?" Falon yayi tsit, baka jin sautin komai, ƙarar gudun A.C, sun yi cirko-cirko suna kallon Nabila. Tuni ta fashe da kuka, jin yadda maganganun Abba, ke dukanta. Abba ya ce "Nasir ya gaya mini komai, da duk bana yadda, yanzu sakamakona kenan a wurinki ko? Sakamakon tarbiyya da ilimin da na baki kenan, ki ƙare a ɓoye mai laifi, azo kama shi a haɗa da ke, ki tozarta ni ki zubar mini da mutunci" Cikin ƙulewa mama ta ce "Wane sakamako ka ke saka ran samu daga tsintacciyar mage, ai ba zata taɓa mage ba, shiyasa nayi ta ƙoƙarin ankarar da kai tun a baya, uban wani ba ya zama na wani, yanzu duk da fifikon da ka nuna mata, bai hanata nuna maka, ita 'yar kunama ce ba, duk gidan nan babu wanda yake janyo maka magana sai ita, yayanka suna zaune lafiya amma ita kullum cikin ɗaga mana hankali take" Baba magajiya ta ce "A'a fa, dan Allah ki sassauta maganganun nan, sun yi tsauri da yawa" Nabila kuwa da a zahiri ta nuna tashin hankali da nadama, cikin zuciyarta kuwa babu alamar hakan, ta yakice gumin fuskarta da yake ta tsatstsafo mata ta ce ""Abba ba mummunan sakamako bane ba, abin da ka tarbiyyantar da ni a kai ne, gaskiya ita ce nake tsaye a kai. Yakamata ayi mini adalci aji ta bakina, ba a goyi bayansa kawai ba ace ni ce bani da gaskiya ba. Wallahi Abba ni ba bibiyar yan iska nake ba, aikina kawai nake yi". Mama ta ce "Har wata gaskiya ce da ke.... Abba ya ɗaga mata hannu, ya dakatar da ita, ya ce "Ya isa haka, ki tashi ki je, bana ko son ganinki, ki je ki yi abun da ki ke ganin shi ne dai-dai, tun da a kan gaskiyar ki kike" Cikin tashin hankali ta ce "Abba baka son ganina fa ka ce, me aka gaya maka har haka a kaina ya sanya ka yanke mini wannan hukuncin " "Abun da ki ka aikata aka gaya mini, muddin kina neman zaman lafiya da gudun ɓacin raina, dole ki bawa ɗan uwanki cikakken haɗin kai, ya gudanar da aikinsa, ki fita daga wannan lamarin, kafin a saka ki cikin masu laifi a kama da ke. Duk wahalar da yaron nan yake yi, kina ji kina gani, amma kika ja bakinki ki ka yi shiru, har barazana ake yi masa na kora, muddin bai kama mutumin nan ba, amma ki ka zagaye ki ka je ki ka ƙulla alaƙa da shi, kin fara bani tsoro Arfa" Cikin matsanancin tashin hankali ta ce "Amma Abba ni kuma menene makomata? Yakamata ka ji ta bakina abba, na karɓi aikin nan ka fahimce ni Abba" Bai tsaya sauraronta ba ya ce "Sai dai kin nuna mini ba ni na haife ki ba, na gode" yayi gaba zai bar falon. Cikin tashin hankali, ta riƙe ƙafarsa ta ce "Haba Abbana, idan har zan rayu kana fushi da ni, me yayi mini saura a duniya? Ka yi haƙuri zan yi abun da ka ce" ta yi maganar tana kuka mai ratsa zuciya, tana sheshsheƙa kamar ta shiɗe, amma ya fizge ƙafarsa yayi gaba. Yana bari falon, tamkar su cinyeta ɗanya, suka yi kanta da surutu, kowa na tofa albarkacin bakinsa. Tashi ta yi tsaye, ta goge hawayenta, cikin ko in kula, ita ma ta bi wata hanyar ta bar musu falon, cikin sigar kwa ci kanku. Ɗakinta, ta shiga ta buɗe drower, ta fito da wasu takardu ta zube su a kan gado, ta kunna system ɗin ta da take caji a gefen gadon, lokaci guda kuma ta ɗauki wayarta tana dannawa. Jin motsin mutum a bayanta, ya sanya ta waiwaya da sauri. A tsaye ta ganshi bakin ƙofa, fuskarsa babu walwala balle annuri. Mayar da hankali ta yi, za ta cigaba da danna wayarta, Nasir ya tako zuwa gabanta, ya tsaya ya ƙare mata kallo sannan ya ce "Kin shirya aikata abun da Abba ya umarce ki ko kuwa? Ina zan kama Viper" Cikin hanzari ta tari numfashin sa ta ce "Ban ce shirya ba, kuma ba zan shirya ba, daga nan har gaban abada,ka je can ka neme shi, yaya Nasir ka fita ka rabu da ni dan Allah". Cikin matuƙar mamaki yake bin ta da kallo, "Yanzu duk kukan da ki ka yi a falo, ƙarya ki ke yi kenan?" A hasale ta ce "Ina ruwanka, idan ma kukan ƙarya ne ko na gaske, ka yi aikinka in yi nawa. Ba dai ka je ka gaya masa ƙarya da gaskiya abun da ka ke so ba? Shikenan, amma kar ka sake yinƙurin shigar mini aiki, idan ba haka ba komai yana iya faruwa, wallahi ba zan fasa abun da na yi niyya ba, idan kuma ka cigaba da takura mini, zan baka mamaki ka taka a hankali kar ka faɗo cikin aikina" Hannu ya saka, ya ɗagota daga kan gadon ya ce "Menene zai faru, wani irin mamaki zaki bani? Me zai faru nake son ki gaya mini. Kina da hankali kuwa Nabila? Kin san doka amma kina taka ta yadda ki ke so? Da me ki ke taƙama ne haka? Sai da na zauna na nutsu, nake tunani, kenan duk hanyoyin da nake bi, dan na samu na kama mutumin nan, ke ce ki ke toshe su ko? Ki ke taka doka yadda ki ke so Nabila" Ta waro masa idanunta ta ce "Doka ko? Ni  iya takata na yi, kai kuma cin zarafinta ka ke ƙoƙarin yi, ka ƙyale ni babu ruwanka da ni, ka yi naka aikin na yi nawa duk wanda yayi galaba shikenan. Idan ka ga dama ka je ka sake gayawa Abba abun da duk yayi maka a kaina, wallahi babu gudu babu ja da baya, ban fara dan ina saka ran dainawa ba, ba tare da na yi nasara ba. Ka rabu da ni muje a kan Sharrin da ka yi mini, ina bin ɗan daba a waje" hankaɗata yayi kan gadon, yana wani irin huci, zuciyarsa na yi masa zafi, yayi wata irin ƙwafa yana bin ta da kallo. Cikin hanzari ya fice ya bar mata ɗakin, saboda idan ya cigaba da tsayuwa, zai iya yi mata abun da ba shikenan ba. Ta yinƙura ta tashi zaune tana haki, tana kallon ƙofar da ya fita. Yana fita ta dafe kanta, saboda yadda yake wani irin sara mata, ta kira Sumayya a waya, sai da ta kusa katsewa sannan ta ɗaga. "Salamu alaikum" "Wa'alaikum Salam, sumayya dan Allah kina ina ne?" "Gida, ban daɗe da dawowa ba ma" "Dan Allah idan kin huta ki zo gida, ina son na ganki, ina cikin matsala ne, ba zama a bari na fito ba" "Subhanallah, wace irin matsala kuma?" "Ni dai ki zo dan Allah" "Shikenan, bari na canza kaya na zo kawai" *** Tamkar an ɗora masa gingimemen dutse a kansa, haka ya buɗe idanunsa da ƙyar, ya na ƙoƙarin tashi, ya ce "Masa oga kar ka tashi, ka huta tukuna" Madaki ya ɗaga kai da kyar, ya ganshi a dabarsa ya ce "Ya aka yi na zo nan?" "Yaran mai zamani ne, suka kawo ka, suka ce wai gaka nan ajiya, zai waiwayeka, amma oga ya na ganka da ƙafa ɗaya, sai nemanka muke yi da kai da lakwari babu wanda ya san in da kuka shiga?" Ya kalle shi ya ce "Akwai wanda suka san na dawo?" "Eh mana, su fidda na kogo, duk suna nan aka kawo ka, labari ma ya fara zagawa cewar an cire maka ƙafa ɗaya" "Wani taimako nake so ka yi mini, amma bari sai na wartsake, kaina kamar an kunna wuta a cikinsa, kamar ana narka mini ƙwaƙwalwa, bari abun nan ya sake ni" "To shikenan, sannu" ***** Sosai Nabila take yi wa sumayya kuka, tana gaya mata abubuwan da suka faru. "Nabila, shiyasa tun da fari na ja miki kunne, babu wanda zai tsaya ya saurareki balle ya fahimce ki, gaskiya ina bayan Nasir, ko dan rayuwarki, yakamata ace kin ajiye wannan shirmen da ki ke yi, ni babban tashin hankalina haukan da ki ka yi wai son shi ma ki ke yi". "Laifi ne dan ka tsayawa wanda aka zalunta?" "Aka zalunce shi a gidan uban wa, mutumin da ya yi kisan kai? Kisan kai fa yayi. Kuma babban tashin hankalin son sa da ki ka fara yi. Ba zaki taɓa ganin laifinsa ba, mutuncinki ya zube a banza, a din ga yi miki kallon mutuniyar banza, wallahi hukuncin da Abba ya ɗauka a kan ki, yayi dai-dai duk wani abu na shaida ko hujja, ki tattara ki ba wa Yaya Nasir, a kama shi kowa ya wuce wurin, kan ki janyo wa mutane magana, ni ba a kyauta mini ba, da bai haɗa woyoyinki ya ƙwace ba, ya bar ki da su" Ta ƙura wa Sumayya ido, yadda ta ɗauki zafin nan, babu alamar za ta tsaya ta fahimce ta, kawai ta yi mata shiru, ta gama masifarta, ta tashi ta fita. Tayi shiru, gaba ɗaya ta rasa abun da yake yi mata daɗi, ta ji gaba ɗaya duniya tayi mata zafi, rana zafi inuwa ƙuna, ta rasa ina zata kama, wurin wa za ta je taji sauƙi. Gari ya waye, Nabila ta shirya tayi ficewarta wurin aiki, ba wanda ta kula, ta yi ficewarta ta tafi. Ofishin barrister Habib taje, ta jira shi, ta samu wuri ta zauna, tana jiransa. Kallo ɗaya yayi mata, ya buɗe ofishin sa, ya ce mata "Taso" Ta tashi ta shiga, suka zauna, ya kalleta ya ce "Ina jinki yau kuma menene?" Nan ta kwashe komai ta zauna gaya masa. Ya ce "Ai dama na gaya miki, dole ki fuskanci ƙalubale, ki yi haƙuri, komai zai wuce, gobe in Allah ya kaimu kotu zata zauna a kan case ɗin su rahama, sannan zan cigaba da duk wani ƙoƙari na baki dukkanin goyon bayan da ki ke buƙata, amma mu cigaba da addu'a" "To yaya Habib, kai kaɗai ne ka fahimce ni, kotu na yanke hukunci zamu shigar da ƙarar kotu ta tilasta wa bunkure foundation fito da ramma, tare da gurfanar da ainihin wanda ya aikata laifin". "Ki yi haƙuri ƙanwata, nasara na tare da ƙalubale, ina yi miki fatan alkhairi da fatan nasara". A sanyaye ta ce "Na gode" "Amma Nabila, a ina zaki yi generating shaidun da zaki shiga kotu da su, a kan case ɗin Viper? A ina zaki ganshi?" "Na ma ganshi, na riga na tanadi duk abun da nake buƙata, domin fuskantar shari'a" "You can do it my dear, kuma in sha Allah za ki yi nasara, akwai yiwuwar zan je na samu major da kaina, nayi masa bayani" Ta girgiza kai ta ce "No need, kar ka je, hakan ba zai sauya komai ba" Ta miƙe ta nufi hanyar fita, tana duba message ɗin da ya shigo wayarta. "Mu haɗu a garden, idan baki da aiki" Tayi masa reply da "On my way". Yanayin yadda take tafe, tana jefa ƙafa, ya tabattar masa da a cikin damuwa take. Tana zuwa gabansa kawai ta nemi wuri ta zauna, ba tare da ta ce masa uffan ba. Ya samu wuri ya zauna a gefenta ya ce "Ya aka yi ne?" Ta girgiza masa kai alamar babu komai. "Akwai mana, fuskar ki ta nuna" "Kowa yaƙi fahimta ta, Abba yayi zazzafan fushi da ni, wai sai na bawa yaya Nasir haɗin kai ya kama ka, ya je ya gaya wa Abba ƙarya da gaskiya, sam Abba yaƙi saurarara ta, sumayya taƙi fahimta ita ma, barrister Habib ne kawai ya fahimce ni, Vi na rasa ya zan yi, zuciyata zafi take yi mini, Nasir ya cuce ni, ya haɗa ni da Abba" "Yanzu zaki ba shi haɗin kai ya kama ni kenan?" Ta girgiza kai ta ce "Ba zan iya ba, ba zan iya bari a kama ka ba". "Meyasa?" Ta ɗaga kai ta kalleshi ta ce "Ka sani ai" "Ban san komai ba" Cikin basarwa ta ce"Kawai ina so ayi wa matarka adalci ne, kuma a hukunta wanda suka yi maka laifin" Ya ce "Gwargwadon yaya ki ke son yar madara?" "Gwargwadon yadda nake son ka" "Ki ke son wa?" Yayi maganar ƙasa-ƙasa. Kasa jurewa tayi, duk jikinta yayi sanyi, ta kasa kallonsa, gashi ya matso daf da ita sosai. "To ungo share hawayen" yayi maganar yana bata handkerchief ɗin sa. Ta karɓa, amma ta kasa gogewar, ta cigaba da kuka. "Dan Allah kar ki karaya, ina ƙara jaddada miki, da Allah na dogara da ke na dogara, amma idan kin ga matsin yayi yawa, ki bayar da kai bori ya hau, ki bashi dama ya kama ni" ta girgiza kai ta ce "A'a, ba zan iya bari a kama ka ba" tayi maganar tana sheshsheƙar kuka. "To ya isa haka kukan, ga wata 'yar ƙaramar kyauta zan baki" yayi maganar yana sake bata envelope ɗin da ya bata wancan karon. Ta saka hannu ta karɓa, tana goge hawayen, tana buɗewa ƙananan hotuna ta ciro guda biyu, wadda ta yi tozali da ita a jikin hoton ce, ta sakata razana, ta kalli hoton, ta kalli Viper ta shafa fuskarta ta ce "Wace wannan?" "Ni ma ban sani ba" "Yaya zaka bani abu ka ce mini ka ce baka san wace ba? Wannan....wann... Kai wannan ba ni ba ce ba, bani ce a jiki ba, yaushe aka yi wannan hoton ban sani ba? Kai wallahi bani ba ce ba, wacece wannan meyasa take kama da ni" ta yi maganar tana kallonsa, idanunta yake kalla, amma bai yi magana ba. "Kayi mini bayani, ka yi magana wacece wannan" tayi maganar kamar zata zare, tana riƙe rigarsa tana zazzaro masa ido. Ayshercool 08081012143 74 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 *BRIGHT PENS SECOND BATCH* KU KASANCE DA LITATTAFAN BRIGHT PENS A SECOND BATCH, NA ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL). MUTALLAB (NIMCYLUV) ZAYTOON (ZEE KUMURYA) DA HADARIN GABAS (NAZEEFA SABO NASHE) Idanunta yake kallo, jikinsa a sanyaye amma yayi shiru bai yi magana ba. "Kayi magana, ka gaya mini wacece wannan? Bani ba ce a jiki, amma meyasa take kama da ni? A ina take?" Still bai yi magana ba, ƙara tsananta riƙon da tayi masa ta ƙara yi, cikin matsanancin kuka tashin hankali da ƙaraji, take jijjiga shi ta ce "Ka yi magana, ka gaya mini wacece meyasa take kama da ni? Kuma a ina take?" Viper ya ce "Ban santa ba, tsintar su nayi, naga ya dace kema ki gani, ban taɓa jin kin ce kina da yar uwa da ku ke ciki ɗaya ba, amma kamarku ta ɓaci da ita, shiyasa na ga ya dace na baki ki gani" "Ka san wacece, ka saba yi mini wasa da hankali wasu lokutan, Please na roƙe ka, don't play with my emotions, ka gaya mini dan Allah" tayi maganar tana kallon ƙwayar idonsa. Ya ɗan jima yana kallonta, kan ya saka hannu ya cire hannunta daga riƙon da tayi masa, yana riƙe da hannunta ya ce "'yan gidanku yakamata ki tambaya bani ba" "Tayaya zan tambaya? Alhalin a duniya babu abun da Abba ya tsana sama da nayi masa zancen mahaifina, ban san dalilin wannan mummunar ƙiyayyar ba, sun yi abun su ya riga ya wuce, amma ya nesan ta duniyata da mahaifina, duk wata hanya da zata saka na san in da yake, Abba ya tosheta wai ba wani abu da zai tsinana mini. Wani abu ne mai ciwon gaske da yake addabar zuciyata, ka fama mini ciwon da yake zuciyata, kuma ka bar ni a duhu, ka taimaki rayuwata wallahi ko Wacece wannan tana da alaƙa ta kusa da ni" Viper ya ce "How, an ce kowane mutum akwai irinsa guda uku a duniya... "Ba wani guda uku, wannan kamar nice a jikin hoton, kamannin nan sun yi yawa, ka wayar mini da kai dan Allah" "Me ki ke so na ce, duk abun da zan faɗa miki ƙarya zan yi miki, ki je gidan abun da suka ce miki shikenan" Ta fizge hannunta, ta yinƙura zata tashi, jiri ya kwasota ta hau tangaɗi, ya riƙe ta, ta ɗan yi shiru ta samu nutsuwa, ta juya ta bar wurin. *** Ramma kuwa kwana suka yi, Abdul yana juye-juye, ciwon cikinsa ya tashi, ko baccin kirki ba su yi ba, sai bayan sallar asuba ya ɗan lafa masa, ya din ga tofa fatiha da bisimillah tana bashi yana sha. Yana kwance a kan cinyarsa, tana ta shafa masa ruwan tofin a kan cikin, tana shafa masa, ya riƙe hannunta yana mayar numfashi. "Sannu Abdul" ya jinjina mata kai alamar yauwwa. "Wai wannan ciwon cikin, ka dudduba kanka sosai mana, kana likita amma ka din ga wasa da lafiyarka, kalli yadda ka ke shan wahala dan Allah" "Tausaya mini ki ke yi?" Ramma ta ce "Duk rashin imanina, idan ban tausaya maka wannan wahalar ba, ya zan yi, idonka har ja yayi saboda wahala". "Rahama ina ga ciwon cikin nan ne zai yi ajalina, har ƙasashen waje na je, an kasa gano menene" Dummm ta ji ƙirjinta ya buga, jin abin da ya ce, amma ta ce "Dan Allah ka daina wannan maganar, ka din ga addu'a ka cigaba da shan magani" "Rahama baki san me nake ji ba ne, ina shan wahala fa" yayi maganar yana miƙa, tare da lanƙwashe yatsun ƙafarsa, hawaye na bin gefen idonsa, saboda azabar ciwo" "Dan Allah ni ka daina wannan maganar" ya juya yayi ruf da ciki. "Idan na mutu zaki yafe mini?" Ta ce "Wataƙila, ai ni dama bana fatan na je gaban Allah ina neman hakkina a wurin wani, ko wani yana nema a wurina, a duniya nake fatan Allah ya saka mini abun da ka yi mini, da kai da wannan jakar matar"ya yi murmushi ya ce "Hakan ma na gode, alfarma ɗaya da zan nema, dan Allah rahama kar ki zubar mini da cikin nan, ina matuƙar son abun da yake cikinki" "Wallahi sai na zubar tas, sai ya bi rariya, ni ka daina yi mini magana kamar wasiyya wasiyya, dan na tausaya maka" Sai da yayi dariya ya ce "Abubuwa ne suke ta hargistewa Rahama, komai ya cukurkuɗe, ban san ya abubuwan za su kaya ba, ina ta ƙoƙarin baki kariya ne iya yi na, duk da ni mai laifi ne" yayi hamma ya ce "Idan ya lafa sai na ji daɗi, gashi bacci nake ji, ke ma na hana ki bacci" Yayi maganar yana shafo fuskarta, ta saka hannu ta sauke hannunsa, ta shafa kansa ta ce "Kayi baccin, ko ka samu relief" ya juyo yana fuskantar cikinta, da yake shafe a jikinta ya ce "Bari na yi magana da yarona" maganar ta sa tayi daidai da jin motsi a ƙasan mararta. A haka bacci ya kwashe shi, ta zuba masa ido, tana jin tausayin sa, gaba ɗaya ya rikice saboda ita, ta ƙara lura da shaye-shaye da rashin tarbiyya ne kawai yake ingiza shi yake rashin mutunci. "Kayi haƙuri Abdul, amma komai ya kusa zuwa ƙarshe da yardar Allah" ***** Walid ne ya magantu, dan tun shigowar Viper ya lura kamar yana cikin damuwa, ya ce "Mai zamani, ya ake ciki ne? Jikin ne ko wani abun ne ya faru?" Ya numfasa ya ce "Na yi abun da ka ce, Nabila" Walid ya ce "Masha Allah, ya ake ciki?" "Ba ta da masaniya a kan hakan, things are complicated, ta shiga matsala daban daban, ta samu matsala da gidansu, an ce lallai ta bawa ɗan uwanta dama ya kama ni, she's almost alone, kamar ban kyauta ba, na ɗora mata abun da ya fi ƙarfinta" Walid ya girgiza kai ya ce "Ƙaddara ce ta haɗa ku, kuma she's not alone, tana tare da kai, muna cigaba da addu'a in sha Allah, komai zai dai-dai ta, ba ta gaya maka komai game da labarinta ba?" Viper ya girgiza masa kai. "Bata bani ba, amma na bata hoton, na ce taje ta tambayi yan gidansu" "Ina jin alamun nasara, in sha Allah ka kwantar da hankalinka" Viper ya amsa da Allah ya sa. **** Nabila kamar mara laka, ta fito daga wanka, jikinta ɗaure da towel, ta jiƙo kanta da ruwa, idanunta sun yi jawur, saboda ta yi kuka sosai da sosai. Kawai ta ɗaga kai ta ga Nasir a tsaye a ƙofar ɗakin, ta ƙara haɗe rai, ta ƙarasa tsane jikinta. "Nabila, lokaci yana cigaba da ja, kuma ke nake jira, haryanzu baki ce mini komai ba, ki gaya mini in da zan samu mutumin nan, ina ɗaga miki ƙafa ne saboda Abba, kuma nima ina jin nauyin aikata miki hakan" Buɗe wardrobe tayi, ta ɗaukko phant da breziar ta jefo kan gado. "Magana fa nake yi miki" Tayi masa banza, ta ɗaga breziar tana ƙoƙarin fara sakawa. "Nabila wai baki da hankali ne? A gaban nawa zaki saka kaya?" "Ni na kawo ka? Ko ka manta bin maza nake yi? Ba abun da zai hanani saka kayana, ai yanzu ba kunyar wani nake ji ba" Galala ya bi ta da kallo, jakar da ta fita da ita, ta janyo, ta ciro ƙaramar wayarta da take vibrating ta ciro ta ɗaga ta ce "Hello V" "Are you safe?" "Yes Alhamdilillah" "It seems you are bit disturbed" "No at all" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Kin tambaya ɗin?" "A'a, ai bai dawo ba, yayi tafiya ne, ni yanzu ina jiran abun da zai kasance a kotu ne gobe in Allah ya kaimu, and su oga Walid su shirya, zasu kasance cikin shaidun da zamu gabatar a kotu fa" "Shikenan, zan gaya musu" "Yauwwa, gobe in Allah ya kaimu daga kotu zan wuce wurin 'yan sanda, a kan case ɗin ka, Allah ya sa...... "Nabila, wai me ki ka zama ne?" Nasir yayi maganar yana tunkararta zai fizge mata waya, ta ja da baya ta ce "Wallahi ka zo in da nake sai na saki towel ɗin nan, na saki ihu ai kai ka zo in da nake, get out from sight, wallahi Nasir ko me zaka yi ina kan bakana, ni, ko wani kaga zai yi mini ƙazafin da ka yi mini, yakamata ka tare mini, amma ka ɓata ni a wurin mutumin da bani da tamkarsa, wallahi ka cigaba da matsa mini kai ma sai na ɓata maka suna a gidan nan, ka fita daga rayuwata ba ɗan daba ba, ko uban wa zan kare ni naga zan iya. Ka je ka yi aikinka nima na yi nawa, kai ma ai amfani ake yi da kai, ake son kama shi ba dan taimkon al'umma ka ke son kama shin ba, get out please" yadda jikinta yake rawa take nema ta saki towel ɗin, muddin ta saki ba shi da kalaman da zai kare kansa da su. **** Indabo ya kalli Abdul da yake zane yana wasa da mukullin motarsa ya ce "Wai meye ne, na ganka kamar wani mara lafiya?" Ya ce "Bakomai, ka yi haƙuri na san maganar yarinyar..... "A'a, ai ba maganar yarinyar nan zan yi maka ba Abdul, ka yi abun da ka ga dama, yau saura sati biyu ɗaurin aure ko wurin yarinyar da zaka aura duk ka kyauta. Magana ce zan yi maka a kan kuɗaɗen da nake sanya wa a account ɗin ka, balli na nema ya tashi, an naɗa kwamiti bincike a kan kuɗaɗen nan, shi ne nake son ka dawo mini da shi, na mayar kan balli ya tashi asiri ya tonu" Abdul ya yi sororo yana kallon Indabo . "Kake kallona kamar shashasha, ka dawo mini da kuɗi na ce, na mayar musu dama na ɗan jinkirta ne, idan komai ya tafi daidai ayi yaƙin neman zaɓenka da su, amma zan tanade su a kusa, da na ji ƙishin-ƙishin  na mayar da su" Abdul ya ce "To, zan dawo da su" ya tashi ya fita. Bayan fitar Indabo P.A ya shigo, ya samu wuri ya zauna, suka gaisa da Indabo. Indabo ya ce "Yaya me ka gano?" "Eh, ana bibiyarsa gidan sa na lay out, ba kowa a ciki, duk gidajen shaƙatawarsa, baya nan abokansa duk na neme su, na bibiye su, amma babu alamar sun san zancen yarinyar ma, amma na in da yake kwana ne, haryanzu ba a gano ba, ka san wayo ne da shi, wasu lokutan a asibiti yake kwana, amma sannu a hankali ana cigaba da bibiyarsa" "Abdul ban san ya aka yi ya zama haka ba, yanzu idan na matsa tsaf zai yi wani rashin hankalin, yanzu ka duba ka gani, saura sati biyu fa auren sa, amma gaba ɗaya hankalinsa baya jikinsa, idan na matsa masa a kan yarinyar nan hauka zai yi mini, shiyasa nake bin sa a sannu, zai zo hannuna sai ya ci ubansa" P.A ya ce "Distinguish akwai matsala fa" "Wace irin matsa kuma? Kullum cikin kiran matsala ka ke kwanakin nan" Ya gyara zamansa ya ce "Distinguish, yarinyar nan sumayya T ladan, sai buɗa maka aiki take yi, kuma duk yan siyasar nan a kanka ta fi cin kashinka, yanzu wasu matasa daga yankinmu, sun kafa wata ƙungiya suna wayar da kan jama'a, wai za su rubuta takarda kiranye za su yi maka, ka dawo gida babu abun da kake tsinana musu sai kwashe musu kuɗi" Indabo ya kalleshi ya ce "Kai ka taɓa ganin wanda aka yi wa kiranye a Nigeria? Rabu da su, ƙaryar banza ce, yanzu muna da abubuwan da suka fi wannan muhimmanci". P.A ya ce "A'a honorable, kar a fara a kanmu, matasan nan fa da gaske suke yi, ka san yanzu muna zamanin social media ne, har cikin ƙauyuka suke bi, da gaske kiranye zasu yi mana" "Ka je ka haɗa sojojin bakan da muke da su, a basu kuɗi, su je su karemu, da daƙile abun, sannan a saya musu fili a kafafen watsa labarai, su shiga su karemu" P.A ya jinjina kai ya ce "Shikenan, babu laifi za ayi hakan" **** Nabila kusan raba dare ta yi, tana kallon hotunan matashiyar da yake hannunta, ta takura ƙwaƙwalwarta, wurin yin tunani, ko ita ce a jikin hoton, amma ita dai ba ta san lokacin da aka ɗauki hotunan ba, tabbas ta san ta nuna hotunan nan, akwai sabon rikici, sai dai ta shirya karɓar duk abun da zai faru, amma sai ta san wacece a jikin hoton. Gaba ɗaya ta ɗauki gaba da yan gidan, ba wanda take kulawa, ko abincinsu ba ta ci. Ta shirya tsaf cikin uniform ɗin ta, ta shirya ta fice. Nabila ce a tsaye a gaban kotu ta nemi kotu ta bata damar gabatar da shaidun da take da su, wanda ba ta gabatar ba a kotun baya. Kotu ta bawa Nabila dama, Nabila ta taso wata mata, matar ta zo ta tsaya a gaban kotu Nabila ta ce "Hajiya ko zamu iya sanin sunanki?" "Sunana hajara wali" "Wacece ke a wurin rahama?" "Ni mahaifiyarta ce, 'ya ta ce" "Ko zaki iya yi wa kotu bayanin meyafaru" Mahaifiyar ramma, tayi bayani tiryan-tiryan. "Kin san wannan?" Tayi maganar tana nuna mata dattijon. "Eh, tare da shi muka yi ta ɗawainiyar zuwa kai rahama Asibiti" "Shi ne ya dawo ya ɗauke ta?" Ta girgiza kai ta ce "Ba shi bane ba, wancan matashi ne" Nabila ta ce "Yanzu ina rahama take?" Cikin kuka ta ce "Ban sani ba, tun da ya ɗauke ta ban sake ganinta ba". "Kafin ya zo ya ɗauketa meyafaru?" Ta goge hawayenta ta ce "Wata mata ce ta zo ta ce mu karɓi kuɗi, a rufe maganar, na ce ban yadda ba, hakkin 'ya ta nake nema, shi ne bayan ta tafi ya zo ya ɗauke ta, bayan kwana biyu ya dawo ya ce mini na bashi kayanta, ta zama mallakinsa" "Ko zaki iya gaya mana sunan matar?" lauyan gwamnati, ya nemi kotu ta dakatar da Nabila, tambayoyinta na ƙoƙarin ƙetare iyaka. Ya taso zuwa gaban majaifiyar ramma ya ce "Hajiya wanda ya zo ya tafi da itan, bayan ya tafi da ita, meyasa baki sanar da jami'an tsaro ba?" "Na sanar da su, amma suka ce na je gida za su neme ni" "Da basu nemeki ba kin koma?" "Na koma har na gaji, amma babu wani cigaba" "Sai aka neme ki aka rasa, ko sama ko ƙasa" "Bibiyar abi mini hakkin 'ya ta da nake yi, ya sanya aka fara yi mini barazana, shiyasa na bar gidan" ya yi wa kotu godiya ya koma ya zauna. Nabila ta sake komawa gaban kotu ta kalli dattijon nan ta ce "Baba a kotun baya, ka amsa kai ne ka yi wa rahama fyaɗe, shin da gaske kai ne ka yi mata fyaɗe?" Ya girgiza kai ya ce "Cewa aka yi idan na ce bani bane ba, abun da ya samu rahama zai samu 'ya'yana". "Meyafaru ranar da abun ya faru?" "A ranar aka ɗaukko ramma daga ƙauye, akwai ƙanin matar gidan ya zo a buge, ya tambayeni matar gidan sun dawo, na ce masa a'a, amma ya shiga, bayan wani lokaci ya fito ya ɗauki motarsa ya tafi. Sai bayan zulai ta dawo daga sayayya, ta fito tana ihu, ta ce na zo na gani, muka tarar da ramma a kwance a ɗakin girki, cikin jini" Nabila ta ce ta gama tambayoyin da zata yi, mai shari'a ya ɗaga shari'ar zuwa sati biyu domin yanke hukunci. Suka fito tare da barrister Habib da mahaifiyar ramma, da yaran dattijon, ta ce "In sha Allah, mune ke da nasara, hukuncin da kotu zata yanke zata yi mana adalci" Barrister Habib ya ce "In sha Allah, komai ya kusa zuwa ƙarshe" Nabila ta ce "Zai dai zo, burina kawai a wanke baba, daga nan mu ɗora da cigaban shari'a" iyalan dattijon suka din ga yi mata godiya. FEW DAYS BACK Cikin tsananin mamaki, kankarofi yake kallon Nabila. Ya ce "Barrister, ke ce da kanki a office ɗina? Ya aka yi ki ka san wurin nan?" Tayi murmushi ta ce "Ba abun mamaki bane ba, matambayi ai baya ɓata, yau gani a ofishin masu ƙasa" Ya ce "Allah ya sa ba laifi nayi ba aka zo kama ni?" Ita ma murmushin ta yi masa ta ce "Yan sanda ai su ne suke kama mutum" ya bata izinin zama. Ta samu wuri ta zauna ta ce "Na yi sa'a, kana kano baka tafi Abuja ba kenan?" "Eh, ina hutu ne, amma haryanzu mamaki nake yi, yadda aka yi ki ka tako da kanki, ki ka zo har in da nake" Ta numfasa ta ce "Ka san komai dalili ne yake kawo shi" "Haka ne, bari na saka a kawo miki abu mai sanyi" Ta ce "A'a, Alhamdilillah tambayoyi ne nake da su a gareka Yallaɓai" "To gimbiyata ina jinki" "Case ɗin da nake yi, na yarinya da aka yi raping, ashe a gidanka aka yi. Na sake komawa na lura da sunan street ɗin sunanka ne, kuma na tambaya aka nuna mini gidan aka ce naka ne. Abun ya ɗaure mini kai, sai dai na jajje amma ban samu abun da nake so ba, matar gidan ta koreni, kusan sau biyu ma, yaya aka yi haka yallaɓai?" Yayi murmushi ya ce "Waye ya ce miki gidana ne?" "Sir gidanka ne mana, Mu'azzam wada kankarofi street, kuma aka nuna mini gidan aka ce gidanka ne, sir ban yi tsammanin haka daga gareka ba, ɓoye mai laifi a ɗorawa wanda bai ji ba bai gani ba mai gadinka?" "Nabila, ina iyakar ƙoƙarina, am even supporting you, baban yaron nan abokin adawata ne, matata kuma akwai yara a tsakanin mu, bai kamata na tona mata asiri haka anyhow ba" "Amma yarinyar mutane da aka zalunta fa? Maigadinka da aka rufe ba da laifinsa ba fa? Wannan ba hujja ba ce ba, what if ɗanka aka yi wa haka? Haba yallaɓai" "Nabila, lamarin ƙasar nan ya wuce duk in da ki ke zato? Dole sai mutum yana lissafi, amma in tambaye ki mana? Waye ya ajiye miki tarihin Bunkure a Office ɗin ki? Waye ya tura miki message ɗin babar ramma? Duk kina tunanin wannan, ko kuwa kawai sabgarki ki ke yi?" Waro ido ta yi tana kallonsa. "Mayar da idanun madam" Cikin mamaki ta ce "But how?" "Through barrister Habib my dear. Ba zan tona wa yaron asiri kai tsaye ba, saboda ubansa ne tushen lalata shi, ba kuma nayi haka ne dan na ɓoye laifinsa ba, ina jan ƙafa a lamarin ne, saboda ki gano komai a sannu, yadda babu mai zargina, duk da akwai jiƙaƙƙiya tsakanina da ubansa. Mahaifiyar ramma na tare da ni, ni na saka aka ɗauketa, tun kan a illata ta saboda case ɗin nan. Zan haɗa ki da ita, zata yi miki bayanin komai, amma ki daina zargina a kan ɓoye mai laifi, am supporting you, program ɗin ma da ki ke yi am supponsoring the program sweetheart, ki daina zargina please, tabbas a gidana aka aikata laifin, kuma ina iya ƙoƙarina a kai madam. Ki je ki cigaba da aikinki, zan cigaba da ƙoƙarina in taimaka miki" Saroro tayi tana kallon kankarofi kamar sokuwa. "Akwai alamar gajiya a tare da ke, ki je zan saka Habib ya kai ki in da take" "Amma duk tsawon wannan lokacin, kuka rufe ni ka ke yi mini yawo da hankali?" "Akwai dalili ne, amma ki yi haƙuri dan Allah, a dalilin haka aka saka miki wuta a office, aka kusa taka ki da mota, duk dan ina tsayawa ina tsawatar wa ne, akwai hatsari a abun da ki ke yi nesa ba kusa ba, shiyasa nake taimaka miki ta ƙarƙashin ƙasa, amma kiyi haƙuri" ba ta ce masa uffan ba, ta ɗauki jakarta za ta fita. "Ina baƙonki kuwa? Idan kun sake haɗuwa ki ce ina gaishe shi" ta tsaya ta waiwayo ta ce "Wane baƙon kuma?" "Viper" ya amsa mata kai tsaye. "Ka san Viper?" Kankarofi ya ce "Na san shi, akwai labari mai sarƙaƙiya ne, amma kar ki matsa, ki bi a hankali, zai kawo ƙarshen labarin, kamar yadda ya faɗa, a sauka lafiya abar ƙaunata" ba ta iya magana ba, ta murɗa ƙofar ta fice. Tun a hanya ta kira barrister Habib, take yi masa masifa, a kan abun da ya yi mata, ya din ga yi mata yawo da hankali da nuna bai san komai ba. Sai da suka haɗu, yayi ta bata haƙuri, yana ƙara yi mata bayani, kankarofi yayi mata kwarjinin da bata tsigale masa ba, amma ta yi wa Habib ta tas. **** Nabila tana tafe tana kallon hotunan hannunta, ta kira Viper ya ɗaga ta ce "V ina wuni?" "Lafiya ƙalau, ya ake ciki?" "Ina hanya zuwa zan yi" "To, Allah ya kawo ki lafiya" **** Ramma ta tsurawa Abdul ido, ya ce kunun gyaɗa yake so, yana sha yana waya, ya ajiye kofin kunun ya ce "Daddy ni dai dan Allah ka yi haƙuri, wallahi ba zan iya fito maka da rahama ba" Ashariya Indabo ya din ga zabga masa, ya ce "Wallahi zan saka jami'an tsaro su kama ka, su ci ubanka, uwar yarinyar nan ta bayyana a kotu, an ambaci sunanka, duk da ba a faɗi cikakke waye kai ba, ga maganar kuɗi na yi maka, duk ka yi kunnen uwar shegu da ni, Abdul kana son ka gama da duniya lafiya kuwa? Dole sai ka tozarta ni?" "Daddy ba tozartaka zan yi ba, makomar rahama nake dubawa ita ma.... Wata ashar ɗin indabo ya lailayo, kamar ba babba ba, ya gama masifar,  Abdul ya ajiye wayar ya dafe kai. "Kai ma da naci kamar me, ka fitar da ni mana, ko ma me za ayi mini ayi mini, sai ɓoye ni ka ke yi kamar ciwo, ni kaina tun ina masifa har na gaji, haba dan Allah" tsaki ya ja, ya tashi ya bar mata dining ɗin. *** "Abba ya yi tafiya, yau nake saka ran dawowarsa, zan nuna masa hoton nan, na ji mai zai ce, tun da kai kaƙi gaya mini wacece?" "Yaya shari'ar ta kasance?" "Alhamdilillah, babar ramma ta je kotu ta bayar da shaida, ina jin alamar nasara in sha Allah" "Mhmm, a ina aka ganta?" "Ta gudu ne wani wuri ta ɓuya, daga baya da taimakon barrister Habib, muka ganota" Viper ya jinjina kai ya ce "ya nawa, ni ya ake ciki?" "Shiyasa na zo ai" "Ok" "Kamar yadda na fara gaya maka jiya, dole ina buƙatar su oga walid, da wannan bugaggen a kotu su bayar da shaida" "Wane bugaggen?" "Oho ni na san sunansa ma? Amm sannan sai ka yi haƙuri, duk wasu rashin ji da ka yi, sai mun yi exposing ɗin su a kotu" "Rashin ji kamar yaya?" Ta kalleshi ta ce "Kamar yadda ka yi mana, sara suka, ƙulla wiwi black market duk da ka yi" Haɗe rai yayi ya ce "Amma ba prison zan koma ba ko?" "Idan ta kama ai dole ka koma" Ya ce "What? Gaskiya ki yi yadda zaki yi, ba zan koma prison ba, wanda nayi 5yrs fa?" Ta zumɓura baki ta ce "Ni na ɗaureka, sai abun da ya kama kawai, bari na je gidan, na ji wadda zamu yi da su, sai anjima" ***** Nabila ta tafi ɗakin Abba, domin amsa kiran da yayi mata, ta tafi bakinta ɗauke da addu'a, ta shiga ɗakin da sallama, suka amsa ban da Abba da yayi shiru ransa a ɓace. Ta je ta durƙusa ta ce "Abba gani" "Nabila ban isa na gaya miki magana ki ji ba ko?" Tayi shiru ta sunkuyar da kai. "Dole sai kin nuna wa duniya cewa ban haife ki ba ko Nabila? Kin nuna mini iyakata, ban isa na nemi alfarmarki ba kenan ko Nabila? Sai kin tozarta ahalin nan gaba ɗaya ko Nabila?" Ta girgiza kai ta ce "Abba bani da wannan burin, kuma wallahi ba zan taɓa aikata wani abu da zan janyo maka zagi ba. Amma dan Allah Abba a yanzu, ka yi mini wani taimako, saboda zatin Allah kar abun da zan nema ya ɓata maka rai" Ta miƙa wa Abba hotunan, da Viper ya bata, ta ce "Dan Allah Abba wacece wannan? Ni dai na san ba ni ba ce ba, dan Allah Abba ko kana da masaniya a kan ta jikin hoton nan. Abba ya saka hannu, ya karɓi hotunan yana dubawa. Ya gama ƙarewa hotunan kallo, ya ce "A ina ki ka samu hotunan nan?" Ayshercool 08081012143 75 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa https://whatsapp.com/channel/0029Va9QtrY4dTnBYG1hST2VHADARIN *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "A office ɗina na gansu" A take Abba ya fara yayyaga hotunan, cikin kuka ta ce "A'a Abba, dan girman Allah ka gaya mini idan ka san ta jikin hoton, Abba ba ka ga yadda kamaninmu suka ɓaci ba, dan Allah Abba ko sau ɗaya ka nuna mini wani a dangin mahaifina dan Allah Abba" ƙarasa yayyaga hotunan yayi, ya watsa mata cikin matsanancin ɓacin rai ya ce "Ki koma in da aka baki hotunan, su gaya miki koma wacece, ubanki kuma ga hanya nan, ki bar mini gida ki tafi yawon nemansa, yayi miki abun da ban yi miki ba, tashi ki bar gabana kan na tattaka ki, da uban naki ya damu da ke, da zuwa yanzu shi ya nemi in da ki ke". Anty ta ce "Haba major, dan Allah ka yi haƙuri kar ka yanke wannan tsatstsauran hukuncin a kan ta, kayi haƙuri dan Allah " gaba ɗaya jikin Nasir yayi sanyi, ganin yadda take ta uban kuka. Cikin tsawa Abba ya ce "Ki tashi daga gabana, ki tafi ki bar mini gida, ki je ki nemi ubanki, amma ki bar mini gida kar na sake ganinki a gidana" Wata irin ajiyar zuciya ta din ga yi, ta yinƙura ta tashi da kyar, ta bar ɗakin, ta koma ɗakinta ta kifa a kan gadonta, ta fara sabon kuka, shi kuwa Abba wace irin zuciya ce da shi haka? Ko menene a tsakanin sa da mahaifinta, yakamata ace ya wuce, ta san ya gama yi mata komai a rayuwa, yayi playing role ɗin uwa, yayi na uba a rayuwarta, amma duk da haka gurbin ido ba ido bane ba. Baba magajiya ce tayi sallama, ta ƙarasa kan gadon, ta dafa kafaɗarta ta ce "Haba Arfa, ke a rayuwarki ba zaki iya haƙuri da tawakalli ba, tun da ya nuna miki baya son zancen nan ba sai ki haƙura ba, shekara nawa ana abu ɗaya kin ƙi ki gane ki haƙura". Nabila ta tashi zaune, idanunta sun yi jawur ta ce "Baba magajiya" "Na'am arfa" "Kema laifina ki ke gani?" Baba magajiya ta yi shiru tana kallonta. "Ki bani amsa mana, laifi nayi dan na nemi sanin in da mahaifina yake na ganshi ko sau ɗaya? Baba magajiya mahaifi fa, a duniya na san Abba ko baki yayi mini, sai ya kamani, bana nufin yi masa butulci ko tozarta shi, amma ina son sanin babana, baba magajiya dan Allah ina da wata yar uwa ne? Ke kin san komai, hoto aka bani da wata a jiki irina ɗaya da ita sak, ko yar uwata ce, dan Allah ki gaya mini. Ni idan kin san in da zan ga babana ki gaya mini, ko sau ɗaya na je na ganshi na dawo dan Allah" Baba magajiya ta girgiza kai ta ce "Ni ban san komai ba, lokacin da na zo gidan nan, an gama dambarwar da za ayi, na zo, ni bani da wani labari a kan mahaifinki" Nabila tayi murmushi mai ciwo, hawaye na bin fuskarta ta ce "Haryanzu kallon yarinyar da ki ka raina ki ke yi mini ko, shiyasa ki ke tunanin bani da wayo ko? Shekaru ashirin da biyar a doron duniya, ai na girmi ki yi mini wayo baba magajiya, amma shikenan, ai Abban ya ce na je ne nemi babana, zan neme shi kuwa in sha Allah " Baba magajiya ta waro ido ta ce "Baki san gatse ba Arfa?" Nabila ta jinjina mata kai alamar eh, ta mayar da kai ta kwanta. Baba magajiya ta ce "Arfa na san har da damuwar matsi da takura da ake yi miki a gidan nan, ya sanya ki ke damuwa da son ganin mahaifinki, ni dai roƙona da ke, ki yi haƙuri idan da rabo zaki haɗu da mahaifinki ko danginsa, amma dan Allah dan Annabi, kar ki bari ku samu saɓani da  maitama" Nabila ta yi mata shiru, dan gani take yi babu wanda zai fuskanci halin da take ciki. Tamkar zuciyarta Abba ya yaga, haka take jin zuciyarta, idan ta tuna yadda ya yayyaga hotunan nan, sai dai har a lokacin tana ganin hotunan yarinyar mai kama da ita a cikin idanunta. **** Duk da Nabila bata jin daɗin komai na duniyar, jin ta kawai take yi gata nan dai, haka ta cigaba da up and down a kan muhimman abubuwan da ta saka a gaba. Ta sake shigar da koke gaban hukumar'yan sanda, ta nemi su kama madaki da wasu daga cikin yaransa, bisa zargin kisan matar Viper, shekaru shida da suka gabata. Yau tana da program a gidan radio, kuma yanayinta ya nuna wa Sumayya tana cikin matsananciyar damuwa, sai dai ta shigo a ƙurarren lokaci, zasu fara gabatar da shirin, dan haka ba ta samu damar yi mata tambayar meyake damunta ba. Nabila tayi iya ƙoƙarin ta, wurin ajiye damuwa a gefe, suka fara gabatar da program. Sumayya ta kalli takardar hannunta sannan ta ce "Jita-jita ta cika gari, cewa kin shigar da koke gaban kotu, a kan lallai kotu ta hana hukumar'yan sanda kamar shahararren ɗan ta'addan, da addabi wani yanki na garin nan, kuma akw zargi da kisan matarsa, duk da yadda hukumar ta 'yan sanda, take nemansa ruwa a jallo?" Nabila ta kalli sumayya da rinannun idanunta, tayi mamakin yadda sumayya tayi mata wannan tambayar, a tsakiyar program ɗin su haka, saboda ba magana ce da ta fita ba, balle ta ce an yi Jita-jita a kai. Sumayya ma ta tsare ta da ido, alamar tana jiran amsa. Tayi wani irin murmushi ta ce "Ba ɗan ta'adda bane ba, mutum ne kamar kowa, kuma ɗan ƙasa da ya dace ya samu duk wani 'yanci da kowane ɗan ƙasa ya dace ya samu. 'yan ta'adda na yawonsu a gari, an san in da suke, an san in da za a same su, hakkinsa muke nema a kotu, ba shi ya kashe matarsa ba. Na san mutane za su yi mamakin yaya aka yi mai dokar bacci ya ɓuge da gyangyaɗi, amma a bibiye ni a cikin shari'ar da zamu gudanar". "Amma ba kya ganin hakan kamar taka doka ne, zaki yi amfani da damarki ta lauya ki taka doka, ki kare mai laifi?" "Sam, dokar da aka wulaƙanta, da ita nake son yin amfani wurin gyara kuskuren da aka yi. Tayaya mutum zai shafe shekaru babu Shari'a, daga baya alƙali da saka hannunsa da umarninsa da komai, a sake shi bisa doron doka da ƙa'ida, kuma daga baya a zo ana nemansa. Shin wanke shi aka yi daga laifin? Ko kuma akwai wani ɗaurin ɓoye da yakamata a warware? " Tayi maganar tana ƙure sumayya da ido. Sumayya ta kalli agogo, lokaci ya cika, ta na tsaka da sallama da masu saurare, Nabila ta tashi ta fice, tana kammalawa, ta tashi ta bi Nabila, amma tuni ta ja motarta ta bar wurin. Ta koma tana sauke numfashi, kiran kankarofi ta gani, ta ɗaga wayar suka gaisa, ya ce "T ladan, meyasa ki ka yi wa Nabila wannan tambayar a tsakiyar program?" "Sir nayi ne, dan tun yanzu ta kare kanta a wurin mutane, kafin abu ya bayyana su yi mata kallon, maciya amana mai fuska biyu " "Sumayya waye ya gaya miki ana iya wa ɗan adam ne? Ba a taɓa iya wa mutum, dan haka ki kiyaye gaba, yayi wuri ki fallasa abun haka gaba ɗaya, amma babu laifi, baki yi kaifi ba, hakan zai ƙara mata ƙaimi" Sumayya ta ce "Ok sir, na gode" ta ajiye wayar ta yi shiru, ita a zahiri tayi hakan ne, ko Allah zai sanya Nabila ta ji nauyin dubban al'ummar da suke goyon bayanta, ta sassauta koma ta haƙura da batun Vipern nan, amma ba ta ga alamar hakan a tattare da ita ba. Abbu kuwa a zabure ya miƙe tsaye, jin program ɗin da yayi, shi ba wani ma'abocin jin radio bane ba, yau kawai ya kunna yana saurare, ya ji shirin ya ƙayatar da shi, haka zalika muryar barrister, kamar sananniya ce a gare shi. Sai dai jin sun yi maganar Viper, ya sanya ya tashi a kiɗime, tare da ɗaukar radion ya fito tsakar gida. Rahila ta ce "Ya dai na ganka a firgice haka?" "Wani shiri na gama saurara, wata lauya ta shigar da koken kotu ta hana kama Aminu, ko gidan radiyon zan je, wataƙila su sun san in da yake" Ta kwaɓe baki ta ce "Ina rabaka da sabgar yaron nan, idan sun san in da yake me zaka yi masa? Salon ka sanya kanka a masifa, wanda ake nema ruwa a jallo da laifin kisan kai? Ka ganshi ka yi masa me? Guduwa fa yayi daga gidan yari" Ya ƙura mata ido, kawai ya girgiza kai, ya kashe radion ya fice. **** Nabila tana driving, wani abu ya tsaye mata a maƙogwaronta, kukan ma gaba ɗaya ta kasa saboda baƙin ciki da ɓacin rai. Katafaren gate ɗin aka buɗe mata, ta shiga da motarta, tayi parking, ta sauka ta nufi cikin gidan. A falo ta tarar da mahaifiyar ramma, tana ganin Nabila, ta tashi da fara'arta, tana yi mata sannu da zuwa. Nabila ta zauna cikin yaƙe, suka gaisa, kamar kullum yau ma mahaifiyar ramma, kallon Nabila take yi, kamar ta haɗiyeta, ita dai ban da an yi mata gargaɗi, da tuni ta faɗi abun da yake ranta, dan ta tantance abun da take tunani, sai dai an gargaɗeta a kan aikata hakan, dan haka ta ja bakinta ta tsuke. "Mama ina fatan dai babu wata matsala ko? Ki cigaba da haƙuri, in sha Allah an kusa dawo miki da ramma, kuma hujjoji nake son kammala tattarawa, na gano ainihin mai laifin, za a gabatar da shi a gaban kotu, idan da wani abu ki gaya mini" Ta girgiza kai ta ce "Ba wani abu, ina ta godiya Ubangiji Allah ya baki nasara, na gode sosai da sosai da ke da Alhajin da ya taimake ni, ina godiya Allah ya biya ku, ya ƙara miki zaman lafiya da mijinki" Nabila ta ce "Ai ba mijina bane mama" "A'a ba Alhajin ba, Aminu" Cikin mamaki Nabila ta ce "Aminu kuma? Nifa ban taɓa aure ba, ba ni da aure" tayi maganar tana murmushi. Babar ramma ta ɓoye mamakinta, kar kwaɓarta tayi ruwa ta ce "Au, ai na zata kina da aure ne, Allah ya kawo miki nagari, ya baki mai sonki da gaskiya, Allah ya tsaya miki, kamar yadda ki ke ta ƙoƙari a kanmu" Nabila ta ce "Amin mama, dan Allah a cigaba da yi mana addu'a, addu'aeku, ita ce ke tasiri a rayuwarmu" Maman ramma ta ce "In sha Allah, addu'a yanzu aka fara" Nabila ta ce "Na gode sosai" ta tashi ta nufi hanyar fita, babar ramma ta bi ta da ido, dan ranar farko da ta fara ganin Nabila, ban da an gaya mata kafin ta zo, an yi mata bayani, da babu abun da zai hanata kurma ihu, ta ce taga gawa. Tana driving sannu a hankali, ta tsaya ta sai abun da zata ci a gida, dan ba sabgar su take shiga ba. A harabar gidan, ta wuce Nasir, ya zuba mata ido, duk ta bi ta rame, saboda ta saka jaraba a ranta, ko kallonsa ba ta yi ba ta wuce. Duk sai ya damu da ramar da ya ga tayi, amma yana nan a kan bakansa sai ya kama Viper, ko zata mutu dan haushi. "Ga agolancin ga yawon ta zubar, ga ta'addanci, gashi an gandame an riƙa a gida babu aure, abun bai yi miki yawa ba kuwa Nabila" Sauda tayi maganar tana dariya. Ta sake cewa " An baki damar ki gusa ki bamu wuri, saboda baƙin naci, kin liƙe mana a gida, tun da ba zaki tafi ba, ki iya kanki, muna son ubanmu, ba zaki kashe mana da baƙin cikin ki a banza ba" Nabila ta tsaya cak, tare da murnar Sauda ta takale ta, ko banza ta rage zafi idan ta yaɓa mata magana. "Ke da ki ke son uban naki, sai gashi kin gagara zaman aure, kin ƙi karatu balle hankalinsa ya kwanta. Ai sauda zaki yi mini gorin aure ne, a lokacin da ke ki ka iya zama a gidan naki mijin. Kuma karki manta da ni agola ce mai 'yanci, a dalilina igiya biyu aka sauke wa babarki ta aure, idan ku ka cigaba da matsa mini, ragowar ɗayan ma sai na tsinketa, sai ku ji daɗin zawarci tare ga uwa ga 'ya. Yawon ta zubar kuma, ina da abun bayar wa yayi mini rana, kema idan ki na so ki bayar nonsense" Sauda ta tashi a ƙufule, Nabila ta ce "Kin san dai ba dakuwa zan yi ba, dama koma wa ki ka yi ki ka zauna" Sauran wanda suke wurin, suka tuntsure da dariya, dan yadda Sauda ke zuba mulki da rashin mutunci a gidan nan, Nabila ce kawai maganinta. **** Cikin mamaki Abdul ya ɗago ya kalli indabo, saboda marin da ya kwaɗa masa. "Ina na kai mini kuɗi Abdul?" Abdul ya yi shiru yaƙi magana. "Ka gaya mini in da ka kai mini kuɗi, kafin na tattaka ka a wurin nan? Yarinya da ka fito da ita, da kar ka fito da ita, matsalarka ce, ba zaka kashe ni da ɓacin rai ba, sai na samo wani wanda ba zai watsa mini ƙasa a ido ba, ina ka kai mini kuɗi?" Mahaifiyar Abdul ta ce "Abdul wai ba magana ake yi maka ba? Ina kuɗin da ya zuba a account ɗin ka, da sunan campaign kuma ya muka yi da kai a kan yarinyar nan?" Abdul ya numfasa ya ce "Na yi wa 'yan garin su rahama gyaran makarantu da hanyoyi, na yi musu boreholes, sai kuma registration da nayi mata na karatu bar zuwa jami'a" ya faɗa kai tsaye. Salallami suka hau yi, da tafa hannu. Indabo ya ce "Abdul, kuɗin ka kwasa ka ƙarar a kan garin yar matsiyata da karuwa?" Ya girgiza kai ya ce "Daddy ba karuwa ba ce ba, koma menene ni ne mai laifi, fyaɗe nayi mata, nayi hakan ne, dan na goge laifina" A fusace Indabo ya rufe shi da duka, ga ƙiba ga hawan jini yana fama, a take ya hau haki, da kyar P.A ya janye shi daga jikinsa. "Ƙarya ma kake yi, ka fito mini da kuɗina, sai na yi seazing ɗin asibitocinka, da duk wata kadara daka mallaka, da wadda na mallaka maka, ni zaka tonawa asiri, wallahi baka isa ba, kuma zan saka a nemo mini yarinyar ko ina ka kai ta, zan yi maganinka daga kai har ita". "Dan Allah daddy kar ka cutar mini da ita, ba tayi laifin komai ba, ni zaka hukunta" Ashariya ya din ga zabgawa Abdul, yama rasa me zai yi, kuɗin da suka yi sama da faɗi da su, domin campaign bisa ga yarjejeniyar idan an yi nasara zasu mayar da kuɗin da uwar riba, ga balli na neman tashi, dama kuɗin mutane ne na wasu hukumomi a ƙasa, ga balli na neman tashi, kuma Abdul ya yi masa hauka. P. A ya ce "Kayi haƙuri, kar ka je wani abun ya sameka, ka rabu da shi, zamu san abun yi, mu fara kashe case ɗin can na gaban kotu tukuna". "Na fara tunanin anya Abdul ɗa na ne? Ƙiriƙiri ya zaɓi mace a kaina, ni zai tozarta?" P.A ya ce "Jarabta ce da kuma ƙuruciya ke damunsa" "A shekara talatin da shidan ne ƙuruciya?" P.A ya din ga bashi haƙuri yana lalaɓa shi, Abdul kuwa tunu yayi ficewarsa. ***** Madaki na zaune a cikin ɗaki, ya din ga jin hayaniya, da iface-iface ana sara suka a ƙofar gidan da yake. Wani daga yaran sa ya shigo da kyar, ya ce "Madaki, yan ƙofa ne fa suka zo gidan nan, muna ta fama da su, sai ƙoƙari suke lallai sai sun shigo gidan nan, su sareka" Madaki ya tashi ya ƙwalalo ido, sai dai kan yayi magana, sun faɗo gidan, sun kai su bakwai, suka zo ka hau shi da sara da suka, wasu na waje na faɗa da yaran madaki. Duk da akwai ƙarfin zuciya, yana ta ƙoƙarin kare kansa, amma sai yaji jikinsa kamar an canza masa wani, duk yayi wani iri babu ƙwari, suka din ga saransa, ƙarshe suka janyo shi daga cikin gidan, suka din ga jan sa a ƙasa tamkar abun banza, duk da iya ƙoƙarin da yaransa suka yi, su ƙwace shi, amma abu ya ci tura, tsofaffin yaran Viper, da yan unguwar su, da ya din ga shiga yana addabawa ya hana su sukuni, su suka yi gangankon ɗaukko shi, suka yi masa laga-laga, suka din ga yawo da shi, lungu da saƙo, daga ƙarshe da ƙyar jami'an tsaro suka kawo masa ɗauki, suka tarwatsa matasan, suka ɗauke shi a galabaice, dan ba su zaci yana raye ba, suka kai shi Asibiti. ***** "My Abdul" ta yi maganar tana murmushi, cikin hanzari ya ɗago, dan bai zaci daga bakin ramma maganar ta fito ba. "Meyafaru ne? Gaba ɗaya na ganka a cikin tashin hankali?" "Rahama abubuwa sun ƙara cakuɗe mini, barin ƙasar nan zamu yi" Cikin mamaki ta ce "Mu bar ƙasar nan, mu je ina?" "Rahama abubuwa ba zasu tafi yadda na tsara ba, zamu bar Nigeria" "Ban gane ba, uwata fa?" Abdul ya ce "Zan saka a kawo miki ita, yanzu visa za ayi miki, amma sai na fara barin garin nan da ke" "Abdul, ni fa gani nake wannan guje-gujen, duk ba zasu kaimu ba, kayi haƙuri ka yi abun da mahaifinka ya buƙata mana" Ya kalleta ya ce "Na kai ki kotu ki gaya wa duniya, ni ne nayi miki fyaɗe? Ba wannan ne ya dame ni ba, abun da zai biyo bayan shaidar da zaki bayar shi ne abun jin, dan haka ki nutsu kiyi abun da na ce kawai" Murmushi ta yi masa da ita kaɗai ta san ma'anarsa, ta wuce shi ta tafi kitchen. **** Daga Naja'atu har Indabo fuskokinsu ɗauke da damuwa, Bunkure tayi ƙwafa ta ce "Gaba ɗaya hankalina a tashe yake, lallai gaskiyar hausawa, ɗan hakin da ka raina, shi ne yake tsole maka ido, yarinyar nan dai ta dage sai ta ga bayana, idan asirina ya tonu, ban san wane irin kallo zan yi wa al'umma ba. Abdul duk shi ya janyo wannan abun. P.A ya ce "Duk ku kwantar da hankalinku, babu wani abu da zai faru, kamar yadda ka yi umarni, dattijon nan zai shiga silent, yanzu uwar yarinyar ta rage, ita muke binciken in da take, kuma ita ma zamu ganota in sha Allah, Abdul ma muna daf da gano, wurin da ya ɓoye yarinyar nan" Indabo ya girgiza kai ya ce "Ban san in da Abdul ya koyi wannan baƙin taurin kan ba, magana ta fito fili, an ce a binciki ministocin da muka ƙulla harƙallar kuɗaɗen nan da su, na san kuma dole sai sunana ya fito, wai ya kwashe kuɗin nan, ya yi wa yan ƙauye ayyukan raya ƙasa, na rasa uban abun da ya samu a jikin yarinyar talaka mara galihu, ya nace mata take abun da ta ga dama har haka" Bunkure ta sauke numfashi ta ce "P.A ya batun barrister Nabila?" "Kamar yadda na gaya muku, sponsiring ɗin ta ake yi, na gwada sakawa a kamo mini ita, amma hakan ya gagara akwai jami'an da suke bin ta, wanda ba san suwaye ba, kuma da alama ita kanta ba ta san suna bin ta ba" Indabo ya ce "Kar ku ja da nisa, kankarofi ne, babbar buƙatar sa ya ga ya kai ni ƙasa, ya rama abun da nayi masa, kuma yayi kaɗan". ***** Nabila na zaune a ɗakinta, tunanin ma ta rasa wanne yakamata ta yi, kawai ta ga Nasir ya shigo ɗakin, ba ta ko motsa ba, balle ya sanya ran za ta kula shi. "Nabila" Ta ɗaga ido ta kalleshi. "Da gaske ke ki ka nemi a hana kama Aminu Viper" "Eh" ta faɗa a nutse. "Nawa aikin ki ke burin ɓatawa kenan, me nayi miki haka ne?" Ta kalleshi ta ce "Ba kai nake fatan ɓatawa aiki ba, duk wani mara gaskiya sai na ɓata masa aiki. Gaba ɗaya ka canza i miss my old DSP, the only person that understand me" tayi maganar tana tashi ta bar shi a ɗakin. Tana office ɗin ta, tana son zuwa duba jikin malam garba, tana son zuwa wurin 'yan sanda, tana son ganin Viper, ga kuma maganar Abba da ta tsaye mata, da ya ce taje ta nemi ubanta, ta bar masa gida. Kenan Abba ya goyi bayan ɗan sa, shi ma a wannan karon ya nuna mata, gurbin ido ba ido bane ba. Turo ƙofar office ɗin aka yi, ta tashi zaune sosai daga kashingiɗar da tayi, tana tunanin ina ta taɓa ganin baƙon nata. Ya samu wuri ya zauna, suka gaisa, ya ce "Baki gane ni ba ko?" Ta jinjina kai ta ce "Gaskiya dai" "Haka ne, magana na zo mu yi da ke mai muhimmanci" Nabila ta ce "Ok, ina jinka" "Saƙo ne daga wurin distinguish Ma'aruf Indabo, na zo mu yi magana mu fuskanci juna da ke" Nabila ta yamutsa fuska tana kallonsa. "Muna yi miki tayin ki fanshi kanki da kanki ne, kan abun da ba a so ya afku" "Ɗan yi sauri, ina da wurin zuwa" P.A ya ce "Maganar da na zo da ita, ta fi abun da zaki je yi muhimmanci, muna son ki janye shari'ar nan ta batun fyaɗe nan, case ne tsakanin ki da Bunkure, kuma ko yanzu kin cika burinki a kanta, akwai maƙudan kuɗaɗe muddin ki ka aikata abun da na ce" Nabila ta ce "Malam na yi maka kama da shashasha ne? Da Bunkure nake case ɗina, meye nasa a ciki? Bibiyar rayuwata da ya saka aka din ga yi, da ƙoƙarin kashe ni, duk bai ishe ku ba, shi ne zaka zo mini da maganar bunkure? Wallahi idan kaga na bar case ɗin nan, to an hukunta ainihin mai laifin ne, kuma muddin wani abu ya same ni, kai ko mutuwa nayi, ina da manya manyan hujjoji a kan sa, da suke a hannun wakilai ne, akwai wanda za su ɗora, in sha Allah sai na bayar da misali a Nigeria, an fara hukunta masu riƙe da madafun iko, da iyalansu, ba wai doka a kan talaka kawai ba, everyone is equal before the law" "Haka ki ka ce?" "Hala kurma ne kai?" Ya ce "To bari mu gani, yaro bai san wuta ba sai ya taka" "Na santa farin sani, tun da na ɗaukko ƘARFEN CIKIN WUTA, da ya gagari hannaye da yawa" P.A ya kalleta ya ce "Me ki ke nufi?" "Zaka fahimta nan ba da jimawa ba" Yana fita tayi tsaki, ta ɗauki jakarta ta fita, a nan ta bar motarta, ta hau abun hawa ta tafi gidan Viper. Yana tsakar gida, daga shi sai ɗan mama a gidan, suna hira. Sun daɗe suna kallon juna, sannan ta ƙarasa ciki, ta samu wuri ta zauna ba tare da ta ce masa uffan ba. Ya samu abu ya zauna, ya ce "Ya ake ciki, meye labari?" "Ko ka neme ni, kwana biyu ina cikin damuwa da tashin hankali, amma ko a jikinka" Ya tsuke fuska ya ce "Menene?" "Vi" Ya Kalle ta, tare da ɗage girarsa ɗaya. "Ka dubi girman zatin Allah, ka tausaya mini, ina ga ciwon zuciya na daf da kamani, kowa ya ja da baya ya juya mini baya, Abba ya yayyaga hotunan nan ya watsa mini, ya ce naje na nemi ubana na bar masa gida, daga shi har yan gidanmu, babu wanda yake kula ni. Gashi a  tsakiyar program sumayya ta hau yi mini tambaya a kanka, yanzu ta ko ina mutane sai attacking ɗina suke yi a media, saboda case ɗinka, client ɗina malam garba wai ya yanke jiki ya faɗi na je na duba shi, na tarar wai ya samu stroke, yanzu P.A ɗin Indabo ya bar office ɗina da tashi barazanar, kuma haryanzu ka ƙi gaya mini dalilin da ya sanya Indabo yake bibiyata. Na rasa ya zan yi me zan yi ne? Kamar na gaza, ba wanda zan je na samu duk na gaya wa damuwata, dan Allah Viper ka gaya mini wacece ta jikin hoton nan, ina jin kamar ina da alaƙa da ita, tun da ni dai na san ba ni bace ba, dan Allah idan akwai wani abu da ka sani ka gaya mini, atleast na rage wata damuwar". "Na gaya miki ban san komai ba, 'yan gidanku zaki tambaya" "Na gaya maka ba zasu gaya mini komai ba, so kake sai na mutu ban san babana ba, idan kana da yadda zaka yi ka taimake ni dan Allah, ko hakan ne alfarmar da ya rage da zaka yi mini a rayuwa" tayi maganar tana haɗa hannayenta biyu cikin sigar magiya. "Ana kiranki a waya" "Ni ba ta waya nake yi ba, ka taimaka mini dan Allah" "Ki ɗaga wayarki " yayi maganar yana kallon ta. Ta ɗaukko wayar, ta ga lambar barrister Habib ce, ta ɗaga wayar ta ce "Hello" "Na duba office ba kya nan, Allah ya yi wa malam garba rasuwa yanzun nan" miƙewa ta yi tsaye, ta saki wayar, ta tashi za ta nufi hanyar fita, jikinta yana rawa. Cikin zafin nama, Viper ya tashi ya riƙe ta, gaba ɗaya ta gigice, ta ce "Sun kashe shi, wallahi kashe shi aka yi" Ya ce "Waye? Waye ya kashe shi?" "Malam garba, wayyo Allahna, meyasa na karɓi shari'arsa, na janyo ya rasa raywarsa a banza, bani da sa'a wayyo Allah zuciyata" wata irin miƙa tayi, kamar zata zare, ta fara kokowar ƙwace wa daga hannun Viper, tana kallon hanyar waje. Ya ƙara riƙeta ya ce "Abla, tsaya ki ji, ki nutsu" Magana take son yi, amma numfashinta ya din ga sama yana ƙasa, hannunta da ya riƙe, ya din ga jin bugun zuciyar ta da sauri-sauri. Ya ciro wani abu a jikinsa, ya saka mata a gefen wuyanta, gaba ɗaya jikinta ya saki. Ya kalli ɗan mama ya ce "Ka kira mutanen nan a waya, su aiko da mota, a kaita Asibiti" Ɗan mama yayi saroro ya ce "A ina ta ajiye motar tata?" Viper ya ƙura masa ido, ya ce "Au, ammm wasu mutanen?" "A tunaninka duk abun da ka ke yi ban sani bane? Zaka kira su ko ni na kira su?" Ɗan mama yayi wiƙi-wiƙi da ido, cikin tsoro da mamaki". "Am talking to you, and you are looking at me" ba shiri ɗan mama ya ciro waya yana kallon Viper. **** "Abdul yau ka addabe ni, kamar nayi maka dukan tsiya haka nake ji" "Sorry baby, kin san kullum ke ta musamman ce, i so much love the natural you". Ramma ta ce "Wallahi ka isheni, duk ka dame ni" "Wallahi wani mafarki nayi da bai yi mini daɗi ba, ya bani tsoro". Ramma ta ce "Maganin wanda baya addu'a" "Wallahi ina yi, har karatun Alqur'ani nake sakawa fa" Ta ce "To Allah ya bada lada, yanzu ka bani wuri na je nayi wanka, zan yi salla". Ya tashi zaune ya ce "Mu je, daga nan sai ki ɗan dafa mana wani abun, yunwa nake ji" Yayi maganar yana ɗagota, daga kwancen da take. A tsakiyar gado suka din ga ciye-ciye da shi da ramma, suna yi yana tsokanarta, tana gaya masa baƙar magana yana dariya. Tamkar ya mayar da ramma cikin sa haka yake ji, kuma ya kasa ɓoye mata hakan, suka kwanta ya gama damunta, bacci ya kwasheta. Juyi ta yi zata gyara kwanciyarta, ta ga Abdul a zaune, ya saka wayarsa a gaba, ya ɗora hannu a ka, yana wani irin kuka tamkar ɗan ƙaramin yaro. Ayshercool 08081012143 76 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa https://whatsapp.com/channel/0029Va9QtrY4dTnBYG1hST2VHADARIN *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* Tashi ramma tayi, ta ce "Abdul, wai menene meyafaru ne?" Yayi mata shiru ya cigaba da kuka. "Dan Allah kayi magana mana, ko mutuwa aka yi muku?" Yayi mata shiru bai yi magana ba, ta kai hannu zata ɗauki wayar, amma ya janye wayar ya kashe. Kawai ya yinƙura, ya ɗauki mukullin motarsa, ramma ta miƙe ta riƙe shi ta ce "Ina zaka je ne?" "Fita zan yi" "A wannan yanayin da ka ke? Idan wani abu ya sameka fa, dan Allah koma menene kayi haƙuri, zuwa Allah ya kaimu gobe, dan Allah ka haƙura da fitar nan" jifa yayi da mukullin, ya koma ya zauna ya cigaba da kuka. Ta zauna a kusa da shi, cikin damuwa ta cire masa hannunsa da ya rufe idanunsa ta ce "Abdul, kalleni menene wai?" Ya sake sunkuyar da kai, kamar ita ce baya son haɗa ido da ita. A hankali ya kwanta a jikinta kamar ƙaramin yaro, ta rungume shi sosai, tana shafa kansa ta ce "Koma menen kayi ta nanata Innalillahi wa Innalillahi raji'un, zaka samu sassauci in sha Allah" wata irin ajiyar zuciya ya din ga yi, wanda sai da ya bata tsoro. "Rahama" ya kira sunanta da kyar a galabaice. "Dan Allah ko na fuskanci hukunci, kar ki manta da ni, na san koma menene zuwa ki gama karatunki, zan fito" "Tom" ta faɗa a sanyaye, dan wasu lokutan har tausayi yake bata, gaba ɗaya Abdul ya saduda, duk wannan iskancin da rashin mutunci ba ya yin su. "Rahama kin ce mini kina da yaya da ƙani ko? Har su ina son in ɗauki nauyin su" Ramma ta ce "Ba na gaya maka yayana ya mutu ba, sai ƙanina sani" "Da gaske ki ke fyaɗe aka yi masa ya mutu?" Ta ce "Oho ina na sani, ba ka ce mini ba a yi wa maza ba, ni kamar haka na so na ji an ce, wai za a samo masa aiki, yaje Abuja aka yi masa, amma mama ba ta taɓa zama ta gaya mini yadda abun ya faru ba, ko tunawa ba ta son yi, idan ta tuno da shi tayi ta kuka" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Ban san me zai faru ba, amma dan Allah duk tsanani kar ki rabu da ni, ki zama mai yi mini uzuri da tausaya mini dan Allah, Allah ma baya kama wani da laifin wani" Ramma ta ce "Da bana yi maka uzuri, da bana tunanin zamanmu zai zo i yanzu, ka daina wannan kukan dan Allah kunya kake bani" tayi maganar da sigar tsokana. Ya ƙanƙameta ya cigaba da sheshsheƙar kuka. "To ɗan jariri, ya isa haka, cikin dare kawai mutum ya tashi yana kuka, ko ka je ka yi alwala kayi salla". "Ba zan iya ba, ba zan yi karatun sallar dai-dai ba" "Kaga amfanin ibada ko, idan bawa ya tuna da Allah, lokacin da yake cikin yalwa, Ubangiji yana tuna wa da shi lokacin da yake cikin ƙunci, ka cigaba da addu'a, Allah ya yaye maka damuwar ka doctor Abdul yasar" yayi lamo kamar kyanwa a jikinta, ba tare da ya kuma magana ba. **** A hankali Nabila tayi juyi, tana ƙoƙarin gyara kwanciyarta kawai ta ga Viper a zaune a kan kujera, yana danna waya. Ta ƙura masa ido tana kallon sa. "Wannan kallon haramun ne, ki daina yi mini wannan kallon" yayi maganar ba tare da ya kalleta ba. Ko ƙifta ido ba ta yi, ta cigaba da kallonsa. Ya waiwayo sosai yana fuskantar ta, ya ce "Ya aka yi ne? Ya jikin?" Ta ɗaga hannunta, ta kalli drip ɗin da yake shiga, ta ce "Vi" "Mmm" "Ina ne nan?" "Wurin sayar da mutane" yayi maganar yana cigaba da danna wayar. Ta lumshe idanunta ta buɗe, ta ce "Kamar bacci nake yi, kuma kamar a zahiri ne, dan Allah da gaske malam garba ya mutu?" Viper ya ce "Eh, ya mutu" Ta girgiza kai, tana kuka daga kwance ta ce "Ai shikenan, ya mutu bai shaƙi iskar 'yanci ba, ban cika masa alƙawarin da nayi masa ba, da yaya zan kalli iyalinsa? Kullum da shi nake kwana nake tashi a zuciyata, ya mutu da mummunan tabo a zuciyarsa da rayuwarsa, ban cika masa alƙawarin da nayi masa ba, na gaza na kasa" tai maganar tana fashewa da matsanancin kuka. "Ke, wai baki da tawakalli ne? Shikenan ke ba zaki mayar da lamarinki ga Allah ba? Wani ya ce ke ki ka kashe shi ne?" Ƙara sautin kukan ta yi, ta ce "Ya ka ji da aka kashe matarka, ya zuciyarka tayi da aka ƙala maka laifin kisanta? Haka iyalan malam garba suke ji, da wannan ɗacin da baƙin cikin ya mutu, kuma ni ban yadda da wani stroke ne ya kama shi ba, wani abun suka yi masa" Viper ya janyo kujerarsa gaban gadon sosai, ya matsa daf da ita, ya ce "Ki yi haƙuri" ta kalli cikin idonsa ta ce "Kai yakamata na bawa haƙuri nayi alƙawarin saka kotu ta wanke malam garba, a gurfanar da ainihin wanda yayi laifin, amma ya rasa rayuwarsa ina kan ƙadamin aikin, na fara tsorata kamar ba zan iya ba Vi" Ya girgiza kai ya ce "Zamu cigaba da ƙoƙari, ba zamu gaza ba, ba zamu sare ba, zamu yi nasara in sha Allah, idan kina cewa kin karaya, nima karaya nake yi" ta ja wata irin ajiyar zuciya ta kalli rigar jikinsa. "Vi" "Mmm" "Me kake ɓoye mini ne? Ba irin wannan rigar ka yaga lokacin kana Asibiti ba, mai tambarin dragon ɗin nan ba?" "Ki daina saka ido, kina ƙirga mini kaya, son rigar nake yi" hararsa tayi ta ce "Am not kid" "You are" yayi maganar very serious. Wani ne ya shigo ɗakin Nabila, yana shigowa ya ce "Viperrr" ya kira sunan yana jan sunan, tare da dunƙule hannunsa, ya miƙawa Viper, Viper ya dunƙule nasa suka haɗa. Ya ce "Ya madam, ta tashi? Barrister ya ƙarfin jiki?" "Ba sauƙi" ta faɗa tana tura baki. Duka suka kalleta, ya ce "Subhanallah, ba sauƙi fa, garin yaya meyafaru?" Ta nuna Viper, ta ce "Baya son na warke, bai iya jinya ba sam" dariya ya yi ya ce "Maza gumbar dutse, ina Viper zai iya jinya dama, ki manta da shi, zaki samu sauƙi in sha Allah, meyake damunki yanzu?" Ta girgiza kai ta ce "Babu komai, ƙirjina ne yake nauyi kawai" "To ki cire damuwa daga ranki, zai daina in sha Allah" Ta ce "Ok sir, na gode sosai" yayi rubuce-rubuce a file ɗin hannunsa ya fita. "Vi" "Mmm" "Wai ina ne nan? Kuma waye wannan ɗin?" "Asibiti da likita" Nabila ta ce "Ai na san asibitin ne, ina son tafiya ne, zan je na ga malam garba" Viper ya kalleta ya ce "Kina da abun gaya wa iyalinsa ne?" Jiki a sanyaye ta girgiza masa kai. "To sai ki daina maganar zuwa" "To ina son na gaya wa yan gidanmu ina Asibiti, kar a neme ni" "Wa zaki kira? Wanda ya ce ki bar masa gida ki je ki nemi babanki, ko kuma yayanki da yake yi miki bita da ƙulli? Ko kuma sauran yan gidan da suke yi miki kallon yar hana ruwa gudu? Ba wanda ya damu da ke, mutum ɗaya ne, kuma a halin yanzu an gurɓata masa tunani, na taɓa tsintar kaina a cikin wannan halin. Mata guba ne mai masifar dafi da saurin kashe wanda suka hara. Annabi Sallallahu alaihi Wasallam yayi gaskiya, da ya ce Bai bar wata fitina a bayansa da take cutar da maza ba a bayansa sai mata, banda haka me zai sanya mace ta raba ɗa da uba?" Yayi maganar jijiyoyin kansa na kumbura, idanunsa suka yi ja, suka ciccika da hawaye, tuna mahaifinsa da ya yi. "Ni ba guba bace ba, idan ka yi wa dukkan mata ka kira mu da guba, baka yi mana adalci ba, yakamata ko albarkacin jauhar mu ci, ka din ga kallon wasunmu ne gurɓatattu, kamar yadda kuma a jinsinku yake da akwai gurɓatattu" Yayi shiru tare da sunkuyar da kai, saboda sake soso masa wurin da yake yi masa ƙaiƙayi. **** Indabo yana zauna yana karyawa, tare da matarsa, kawai Abdul ya faɗo tsakiyar wurin da suke cin abincin. "Meye haka Abdul, baka iya sallama ba baka iya gaisuwa ba" Indabo ya ce "Ko giyar ka je ka sha, ka yi shaye-shaye ne?" "Na daina shan giya da miyagun ƙwayoyi, tun bayan da rahama ta shigo rayuwata, ta haskar baƙar bayahudiyar rayuwar da kuka tarbiyyantar da ni a kai, kodayeke gara ma ni shan giya ne da neman mata kawai, but am so much disappointed on you, nayi dana sanin kasancewar ka mahaifina. Dama a tsatson talakawa na taso, talakawa futuk sai ya fiye mini wannan mummunar rayuwa da iftila'in kasancewar ka mahaifina" "Abdul, uban naka ka ke gaya wa haka? Duk iya ƙoƙarin da yayi na ƙarar da rayuwarsa wurin ganin ya gina ku, ka zo gabansa kana gaya masa wannan maganar?" "Mummy! Wace irin gina rayuwarmu, gangar jikin da aka gina da zunzurutun haramun da jinin mutane? Haba mummy da alama mafitarki kawai ki ka nema, ya sanya ki ka auri Daddy, wallahi mu 'ya'yanki baki yi mana adalci ba, kuma a yau ba sai gobe ba, zan bar ƙasar nan, na nesanta kaina da ku, tun kafin asirinka ya tonu a idon duniya abun da ka yi ya shafe ni, gara in kalli duniya a hukunta ni da laifin fyaɗe da nayi, da a hukunta ni da mummunan laifin da ka aikata, ga waya nan ka karɓa ka saurari saƙonka" Yayi maganar yana miƙa masa wayarsa, Indabo ya saka hannu ya karɓa, yana dubawa. Wani audio ya fara buɗewa, sai dai jin muryar wanda yayi message ɗin kawai, ya rikita masa lissafi, ya fara gumi hannunsa ya hau rawa. "Wanna saƙon ba naka bane ba, na mahaifinka ne. Duk da ina da access na yadda zan same shi, amma yafi dacewa na tura masa saƙon ta hannunka, sai yafi karɓar sa da muhimmanci. Lokaci yayi da zamu daina buga wasan 'yar ɓuya da kai indabo, zamu yi wasa na ƙeƙe da ƙeƙe, saboda ina daf da barin ramina da nake ɓoye, na cigaba da addabar rayuwar ka ta kowane hali. Idan ka muzgunawa Nabila, tamkar jauhar ka taɓa mini, taɓa jauhar kuwa taɓa zuciyata ne kai tsaye. Dan zan yi wasa irin wanda ka ke so ayi. Ka so ta zama tarkon da zaka yi amfani da shi ka kamani, shi kuma Allah ba azzalumin sarki bane ba. Ɗanka ya yi wa rahama fyaɗe ƙanwar Nura, da ka lalatawa rayuwa ka kashe, ka ɗorawa wani daban, kuma ka bishi ka saka an kashe shi. Abun da baka sani ba shi ne, ina da cikakkiyar shaidar mummunar ɗabi'ar da ka ke aikatawa, ta lalata rayuwar matasa da sunan sama musu aikin yi. Sannan ni na saka aka kama ɗanka Jafar, a Mexico in da ya gudu neman mafaka bayan yayi kisan kai, haka zalika yanzu ma da saka hannuna a mayar da shi amurka. Yanzu haka miyagun ƙwayoyi da hodar iblis ɗin da aka loda maka a jirgin ruwa, za ayi safararsu ta ruwa, za a kama su a gaɓar tekun italy. Kamar yadda nayi maka aike na farko, ina tare da Simon kuma shi ya bani wannan saƙon naka". Jiki na rawa ya buɗe videon, shi ne a cikin videon, yana ta kokowa da Nura guduma, wasu irin ƙarti majiya ƙarfin gaske, suka riƙe Nura, yana kururuwa yana ƙoƙarin ƙwatar kansa, amma abu ya gagara, kuma ba iya fuskar Indabo ba ce a videon, har da wasu daga cikin manya a ƙasa. Da ƙyar Indabo ya iya ɗaga ido, ya kalli Abdul, ya haɗiye wani irin abu mai yaji da ɗaci, ya kasa magana. Abdul kuma ya ƙure shi da ido, yana jiran ya ji mai indabon zai ce. Mahaifiyar Abdul tayi shiru, suka yi tsuru-tsuru. "Na tabattar ba sharri aka yi maka ba, kai ne a jikin videon nan, naga baka buɗe sauran audios ɗin ba, amma ya tabattar da cewa, mutum goma ne suke da videon, muddin ka cigaba da takura musu, sai sun sake shi a duniya, kuma sai an ɗauki mummunan mataki a kanka, babban takaicina me zan cewa rahama, yarinyar da nake nema ta yafe mini, ashe akwai babban aiki a gabana jawur, kai kayi silar mutuwar ɗan uwanta, tayaya mahaifiyarta zata yafe mini ta bari na cigaba da rayuwa da ita?" "Abdul ka cigaba da rayuwa da wa? Tona wa mahaifinka asiri zaka yi? Satin bikinka ya kama kana nufin zaka yi aure kuma ka ajiye karuwa?" "Rahama ba karuwa ba ce, aurenta nake yi, kuma yau zan tattara na bar garin nan da ita, da wannan abun kunyar da ka aikata" Indabo ya ce "Aurenta ka ke yi kamar yaya?" SOME MONTHS BACK. Abdul ne ya shigo, ya tarar da rahama a rakuɓe, a jikin gado, idanu duk sun kumbura saboda kuka. "Wai ba zaki raba kanki da wannan kukan ba? Aikuwa kina tare da wahala, dan kuwa yanzu ki ka fara, tashi ga abinci" Ta ɗago ta kalleshi ta ce "Ba na ci, ka ƙyale ni na mutu, ai tun farko cewa kayi zaka kashe ni, menene na ajiye ni kana tozarta rayuwata, saboda kawai ina 'yar talaka? Talauci ne ya saka na fita aikatau, da burin yin karatu, mahaifiyata ba zata iya ɗaukar ɗawainiyata ba, ban da haka killace ni zata yi a tare da ita, ba zata bari ma ka ganni ba balle ka keta mini haddi" ta yi kneel down ta ce "Dan girman Allah ka kasheni na huta" "Ke naji, kin cika mini kunne da koke-koke, zan mayar da ke" Ta girgiza kai ta ce "Ko ka mayar da ni, ba zan yi daraja ba, abar ƙyama zan zama, kawai ka kashe ni, ka kaiwa mama gawata dan Allah" Abdul ya zauna a kusa da ita ya ce "Ya isa haka kukan, ki ci abinci zan san abun yi" kwanaki biyu, tana jiran ya kashe ta, ko ya mayar da ita amma shiru, gashi tun da tayi ɓarin nan, da ya zo mata zata fara kuka kamar ranta zai fita, tana yi masa magiyar ya daina wulaƙanta mata rayuwa. Cikin marairaicewa ta same shi, ta durƙusa a ƙasa ta ce "Ka ce zaka mayar da ni gida, kuma baka mayar da ni ba" "Rahama ba zan iya mayar da ke ba, zan ta tunaninki ne, kawai na ji ina damuwa da ke, ki haƙura kawai" cikin kuka ta ƙare masa zagi, amma ko a jikinsa. Washegari ya ɗauki Salim, ko saifu bai gaya wa ba, suka tafi gidan su ramma. Mahaifiyar ramma na ganin Abdul, ta tashi cikin ƙarfin hali ta ce "Ina ka kai mini 'ya ta? Ka dawo mini da 'ya ta" Abdul ya ce "Mama masalaha na zo muyi, ɓarna an riga an yi ta, dan Allah ki yi haƙuri ki bar mini ramma, ki bani aurenta" Sai da Salim ya kalle shi, dan bai san abun da zai ce kenan ba. "Allah ya tsare, cuta ka riga ka gama cutar da mu, kai da Allah, amma ka dawo mini da 'ya ta" Ya girgiza kai ya ce "Kar mu yi haka, a rufa wa juna asiri, kun ɗauki aure da muhimmanci sosai, ta ce babu lallai tayi daraja, ƙyamarta za a din ga yi, dan haka ki yi haƙuri dan Allah, ki aura mini ita" "Wallahi ba zan taɓa aura maka ita ba, gara ayi ta tsangwamarmu, zan riƙa a bata na kula da ita, kuma zan cigaba da nema mata hakkinta, har zuwa ƙarshen numfashina" Ya miƙe ya ce "Shikenan, tana gaishe ki, ki kwantar da hankalinki, tana cikin ƙoshin lafiya" ya ajiye mata kuɗi suka fice, ta bishi tana ya zo ya karɓi kuɗinsa amma yayi mata banza suka tafi. Salim ya din ga yi masa masifa a mota "Amma dai baka da hankali ko? Ka yi wa yarinyar fyaɗe, mu zo gaban babarta mu yi rashin mutunci, kuma mu dawo ka ce zaka aureta, wai ma ka gaya wa su daddy ne?" Abdul ya girgiza kai ya ce "A'a, yarinyar ce take bani tausayi irin sosai ɗin nan, virginity is very important to woman's, i took it away just like that, she's very young and innocent, ina jin babu daɗi, na san yadda zan ɓullowa lamarin" Tare da Salim suka cigaba da shige da fice, suka samo wani wan baban ramma, Abdul ya danƙara masa kuɗi, babar ramma bata sani ba, aka ɗaura musu aure, sai bayan an ɗaura ya je ya din ga yi wa babar ramma masifa, wai Allah zai rufa wa ramma asiri, amma tana ƙoƙarin tonewa, da ta samu ma mai kuɗi da kyau kamar wannan ya saurari yar ta ta, a wurin ɗan birni kamar Abdul ai ramma a bar ƙyama ce. Cikin kuka ta ce "Wallahi balarabe ba zai yiwu ba, ban san wani zancen aurar da ramma ba, lokacin da nake wahala ta da ya ta da me ka taimake ni, ina har gonar su ta gado ka cinye". "Oho miki, koma menene rashin iya takaucinki, da son abun duniya ya sanya ki ka kaita aikatau" da kansa ya shiga ya kwaso wa Abdul kayan ramma, ya sake ba wa babar ramma kuɗi, ya ɗauki kaya suka tafi. Suna tafe Salim ya ce "Ranar da asirinka ya tonu ban sanka ba wallahi, ko kuma ka gama abun da zaka yi, salin alin ka sakar musu 'ya" Abdul ya ce "Ban aureta dan na saketa ba, sai dai ayi wadda za ayi" Ya je ya samu ramma, ya kai mata kayanta, da goro da alawa ya ce "Gashi nan, hankalinki ya kwanta an ɗaura mana aure yau" cikin mamaki ta kalleshi ta ce "Aure kuma kamar yaya?" "Ba damuwarki kenan ba? Ke ba zaki auru ba? To an ɗaura yau, yayan babanki wai malam bala, shi ne ya ɗaura mana aure" "Wane irin aure ne babu istibura'i? Cewa nayi ina sonka ne ma?" Ya ce "Meye istibura'i?" "Sai nayi jini uku a addinance, dan tsaftace mahaifata kan ka aureni, tun da zina kayi da ni, kuma ni bana sonka". Abdul ya kalleta ya ce "Allah ya nuna mana wata ukun, kuma ni ina sonki ai, Shikenan an wuce wurin". Ramma tayi kuka a kan wannan wulaƙanci da Abdul yayi mata, da nuna mata tsantsar isa da gadara, ta fara yi masa misbehaving ta daina tsoronsa, amma ko a jikinsa, sai dai zamansu tare ta gane yana da wasu ɗabi'u na tausayi da sauƙin kai, rashin tarbiyya da ilimin addini ne kawai yake ɗawainiya da shi, bai sake nemanta ba, sai da ta cika watanni uku, kamar yadda ta buƙata. Idan tana yi masa masifar ba dan Allah ya aure ta ba, ya kan ce mata "Ba dan ina sonki ba, babu dalilin da zai sanya na zauna da ke watanni uku ina kallonki, kina gindaya mini sharuɗa ina ƙyale ki". **** Mahaifiyar Abdul ta ce "Aure ka yi bamu sani ba Abdul, rashin muhimmancin namu har ya kai haka?" Ya kalleta ya ce "Ko zan mutu ba zaku yadda ku aura mini rahama ba, zaku yi iƙirarin yar talakawa ce, ba tare da la'akari da ɓarnar da na akata mata ba. Kuma sakawa zaka yi a kasheta, sannan mutumin nan da ka saka aka kashe, ba ruwana babu saka hannuna a ciki. Zan ɗauki matata mu bar garin nan, dan Allah kar ka neme ni, takara kuma ka bawa wani, ba zan iya ba" ya ɗauke wayarsa, mahaifiyarsa ta bishi tana ƙwala masa kira, amma yayi waje. *** Viper ne ya shigo ɗakin da Nabila take, tana zaune ya shigo da waya a kunnensa ya ce "Eh na je wani wuri ne, ɗan mama ya dawo gidan nan ne, ya gudu na neme shi na rasa, ya kuma kashe wayarsa" Walid ya ce "A'a bai dawo ba, ko laifi yayi maka ka ce zaka hukunta shi?" Yayi murmushi ya ce "Laifi yayi, kuma duk in da ya shiga zan nemo shi, zamu gauraya da ni da shi"ya katse wayar ya ƙarasa gefen Nabilaya zauna. "Vi" "Mmm" "Wai dan Allah ina ne nan? Ina son na tafi gida ne" "Ai ba zaki koma gida ba, kin zo kenan" Dariya tayi, dan ta zata da wasa yake yi. "Daga fitarka ka sha sigari ko?" "Eh" Nabila ta ce "Au eh, baka jin kunya wai ka amsa ka tsaye, sai ƙauri ka ke yi, ba na son ƙaurin abar nan ko kaɗan wallahi" Ya tsura mata ido, ya girgiza kai ya ce "You can't be her" "Who?" Ya lanƙwasa ƙafarsa ɗaya a kan gadon ya ce "Jauhar, ba ta taɓa nuna warin sigarina da wiwi yana damunta ba, sai dai ta ce ; Master kar a sha da yawa, dan Allah a sha kaɗan, idan nayi shaye-shaye na dawo, ta bani ruwan wanka, ta bani wankakkun kaya, ta fesa mini turare, sai daga baya na fahimci, warin wiwi ne ba ta so, amma bata taɓa yi mini complain ba. Yanzu bana iya shan komai, na yadda ƙwaƙwalwata da lafiyata suna da amfani, ko dan ganin bayan wanda suka cutar da mu. Ke kuwa masifaffiya ce, always angry, ki ka gaya mini ina ƙaurin taba" "Sai na zama irin ta zaka so ni? Gaskiya ba zan iya shiru ba, ni kawai ka daina gaba ɗaya" Viper ya ce "Ai babu wannan maganar tsakanina da ke, na gaya miki ki daina wahalar da kanki" ya yi maganar yana miƙa mata wayarta. Karɓa ta yi tana hararsa ta ga sunan sumayya ta ce "Ba zan ɗaga ba" "No, ki ɗaga baki san me za ta ce miki ba" Ta ɗaga ta saka a kunnenta ta ce "Ina jinki" "Nabila kina ina ne?" "Menene?" "Kawai malama kina ina?" "Ki gaya mini meyafaru? Nayi nisa ne" Sumayya ta ce "Mahaifin Viper, ya zo gidan radionmu, ya ce yana son zai yi magana da ke, na ce masa zan haɗaku, zan yi miki magana" Nabila ta ce "Are you serious dan Allah da gaske?" "Wallahi da gaske nake yi miki" "Shikenan, in sha Allah zuwa gobe in Allah ya kaimu, zan zo zamu haɗu, kin karɓi lambarsa?" "Eh na karɓa" "Shikenan in sha Allah zan zo" ta katse wayar, ta ga wani irin kallo da yake yi mata. "Vi snake, menene? Abunka ne ya zo yana nemana, wataƙila..... "Silent. Kar ki kuskura ki fara, ke gaba ɗaya baki da lissafi, idan wani trap ɗin ne fa?" Yayi maganar cikin hargowa. "Bari na zama kamar jauhar, ba zan biye maka ba ai yanzu, hukuma sai da rarrashi, hadari malafar duniya. Tsakanin ɗa da mahaifi sai Allah. Nifa duk da ina da labarin abun da babanna yayi wa mahaifiyata, fata nake yi na ganshi, haka zaka cigaba da rayuwa ba dangi, kaikaɗai sai su oga Walid, sai kuma Ni" ta yi maganar tana murmushi. "Ka bari mu haɗu da Abbu dan Allah, na san maybe nemanka yake yi, so yake ya ganka, haba sweetheart, namijin duniya, kar ka saka muyi babu, kai ba uba nima haka, kayi haƙuri dan Allah, ka manta da komai My Vi. Magana fa nake yi an yi mini shiru, talk mana, ko sarautar ce ta motsa? Master magana nake" tsigar jikinsa ta mimmiƙe ya juya yana kallonta. "Ban taɓa kallon wani abu na ji ina son shi ba, sai kai Vi, duk a dalilinka na rasa ajina da jin kai na 'ya mace. Gashi ka yi ta hantarata, baka tausayina ko kaɗan. Ɗan nuna mini hoton 'yar madara mana, ko sau ɗaya ne" "Hotonta mai tsada ne, yarinya mai haƙuri da aji" "Ni kuma masifaffiya mara aji, daga nan kuma sai me?" Ya fuskanci kawai kunna shi take yi. Ya ajiye mata wata leda, ya ce "Gashi nan, abinci ne, za a kawo miki kaya" "A'a nifa ban gane ba, gida fa?" Ya miƙe tsaye ya ce "Ba sa buƙatar ki, na fi su buƙatar ki a yanzu, muddin wani abu ya sameki, ni aka jiƙawa aiki" Nabila ta ce "Ban gane ba, garkuwa zaka yi da ni?" "Na ma yi" yayi maganar tare da ficewa. **** Hanklin can gidan su Nabila ya tashi, bayan an shafe kwana na biyu, ba a san in da take ba, Abba ya maze kamar ko a jikinsa, amma hankalinsa a matuƙar tashe yake. Nasir ma ya din ga up and down, haka ma sumayya dan sai da ta gaya wa Kankarofi an nemi Nabila an rasa. Ta gaya wa Nasir cewa, ranar da ta ɓata sun yi waya, bayan la'asar kuma da alama tana cikin ƙoshin lafiya. Nasir ya ce "Abu ne mawuyaci ace barin gidan nan tayi, wataƙila mutanen da take addabawa ne suka sace ta" Aka din ga kiran wayarta, amma a kashe. Kwana na uku, Nasir ya kira wayarta, ta shiga, amma ba a ɗagawa. Dan haka ya saka layin a tracker, ya fara tracking in da wayar take, sai dai ga mamakinsa, wayar tana cikin garin kano. **** Abdul tamkar zai haukace, duk wani lungu da saƙo na gidan ya duba, amma bai ga ramma ba, ya dudduba ko ina da ina, amma bai ganta ba. Ya kira wayarta amma a kashe. Taka jikinsa ya hau tsuma, ya tabattar da cewa Indabo ne ya saka aka ɗauke ta, jikinsa na rawa ya ɗaukko mota ya fito, tare da sakawa a ransa komai zai faru sai dai ya faru, amma sai indabo ya fito masa da matarsa, ko kuma shi da kansa ya tona musu asiri kowa ya huta. **** Nasir yayi mamakin surƙuƙin wurin da yake indicating in da wayar Nabila take, da shi da abokan aikinsa, ƙarshe ajiye motar suka yi, suka din ga shiga wurin da ƙafa, suna cigaba da dubawa. A tsaye suka tarar da shi ya juya baya, hayaƙi yana tashi. Nasir ya ce "Malam waye kai?" Sai da ya ja sakanni, sannan ya juyo a hankali, hannunsa ɗaya da wayar Nabila, ɗaya kuma riƙe da sigarinsa, gaban rigarsa ɗauke da sunansa Viper da hoton maciji a jiki. "Al'amin Viper, ko ka ce mai zamani" Ayshercool 08081012143 77 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa https://whatsapp.com/channel/0029Va9QtrY4dTnBYG1hST2VHADARIN *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA Cikin matsanancin mamaki, Nasir ya cigaba da takawa zuwa gaban Viper, ya ɗan bayar da tazara tsakaninsa da shi. Nasir ya ce "Dama kai ne Vipern?" Ya ɗan kaɗa kai ya ce "Ni ne Viper, abun mamaki ko? Haɗuwar mu biyu, amma baka san ni ne ba, haryanzu ina mamakin wane irin aiki jami'an tsaron ƙasarmu su ke yi, kodayeke ƙulafucin cin hanci ne yake rufewa galibinku idanu, ku danne masu gaskiyar cikinku, ko ku sauya musu ra'ayi domin neman mafitarku kawai" Nasir ya ƙare masa kallo ya ce "Ina 'yar uwata take? Ina Nabila?" Viper ya jujjya wayar Nabila sannan ya ɗagawa Nasir ita ya ce "Baka buƙatar yi mini wannan tambayar, tun da ka samu wayarta a hannuna" "Tana ina?" "Tana wurina ƙarƙashin kulawata, na fiku buƙatar ta, ina buƙatar ganinta a raye domin nayi surviving, dan haka za ta cigaba da zama a ƙarƙashin kulawata, har zuwa lokacin da ya dace" A fusace Nasir ya ce "A matsayinka nawa, am arresting you, ba zan bar wurin nan ba, sai na kama ka" Viper ya kalle su gaba ɗaya 'yan sandan su biyar ɗin ya ce "Bisa wace dokar? Ko bisa umarnin indabo da ka karɓar wa kuɗi, zaka kama ni?. Viper ya zaro takarda a aljihunsa ya ce "Na sami wannan takardar yau da safe, kai ma kuma ka je ka bincika, kotu ta hana hukumar 'yan sanda da kowace hukuma kama ni, har sai an kammala bincike, dan haka ba ka da wannan ikon, hannunka bashi da ƙwarin ɗaukar ƙarfen cikin wannan wutar, ba zaka jure ba, muddin ka taɓa kuwa, zaka yi ƙunar da zata yi dalilin rabaka da hannun" Nasir ya fizgi takardar hannun Viper, jikinsa na rawa, ya hau karantawa, tabbas Viper da gaske yake, kotu ta bayar da umarnin hana kama shi. Nasir ya riƙe takardar, ya zaro bindiga a jikinsa, ya ce "Idan kuma na kashe ka a wurin nan fa, waye ya sani?" Viper ya nuna masa mutanen bayansa ya ce "Ku 'yan sanda ai ba dukkanku ne masu amana ba, wane tabbaci ka ke da shi cewa mutane huɗun nan na bayanka, ba zasu tona maka asiri cewa ka kashe ni ba? Beside kana sakin bullet ɗin bindigar ka, kaima za a kashe ka, tunaninka a banza na zo nan na jiraka? na san kana tracking ɗin wayar, shiyasa na jira ka zo ka iskeni" Ya ciro ID card ya ɗaga wa Nasir ya ce "I am an NIA officer, and also a former thug, ni ba da bindiga zan yi maka illa ba, ƙarfe zan saka maka, a ɗan daba na zan yi maka illa, ba jami'i ba. Sauke bindiga Nasir yayi, ya ce "NIA officer how?" "Kamar yadda ka gani. Maganar Nabila kuma, bari na gaya maka wani abu, na san kana sonta amma ta haramta a gareka, muddin ina ganin fuskar matata a ta Nabila, aurenta ya haramta a gareka, ba kai ba kowa ma. Nabila tana wurina, kuma zan mayar da ita wurin mahaifinta, wannan shi ne tukuicin da zan yi mata, bisa ga jajircewarta da ceto rayuwata" "Mahaifinta like how? Me ka ke nufi da hakan?" "Hoton da na bata, ta kai muku ku yi mata bayani, amsar da ku ka bata, ta sanya na yanke shawarar yin abun da ya dace" Nasir zai kuma magana, wani ya ƙaraso wurin da babur, sanye da riga mai tambarin NIA (National Intelligence Agency) Viper ya hau babur ɗin, suka bar wurin. Dafe kai Nasir yayi, yana tunanin wannan wane irin rikitaccen al'amari ne, tayaya riƙaƙƙen daba ya zama jami'in cibiyar samar da bayanan sirri da leƙen asiri? Ya aka yi kuma ya san mahaifin Nabila, anya wannan duk ba wata shiryayyiya ba ce ba?. "DSP yakamata fa mu bar wurin nan, ni gaba ɗaya ban yadda da mutumin nan ba, i don't think we are safe here" bai ce uffan ba, ya yinƙura ya tashi suka bar wurin. **** Gida Nasir ya nufa, a wahale, cike da damuwa da tashin hankali, yama rasa ta ina yakamata ya fara, meyakamata yayi. Ya za ayi hukuma kamar wannan, ta bar jami'inta yana tafka rashin mutunci son ransa. Yayi shiru yana tunanin yadda wasu abubuwan suka din ga faruwa, ya aikata laifi, amma a bi a goge duk wani trace da zai nuna shi yayi, ko kuma a gano shi. Babban abun da ya ƙara baƙanta masa rai, shi ne umarnin kotu, na hana kama Viper, ana tuhumar mutum da laifi, har na kisan kai, amma ace kotu tayi umarnin dakatar da kama shi a kan me?. A ƙofar gidan su, ya tarar da manya-manyan motoci har da na 'yan sanda, cikin sauri ya yi parking, ya shiga cikin gidan domin ya ga mai yake faruwa, baba magajiya ta sanar masa major ne yayi baƙi. Hankalinsa bai kwanta ba, ya nufi ɗakin Abba, dan tabattar da abun da yake faruwa. Ya tarar da Alhaji mu'zzam kankarofi, tare da wasu jami'an tsaro, da kuma Abba a falonsa. Abba ya ce "Yauwwa, ƙaraso Nasir" ya ƙarasa ya shiga, ya zauna suka gaisa. Abba ya ce "Ka gane wannan ai ko?" Yayi maganar yana nuna masa Alhaji mu'azzam. Nasir ya ce "Eh ya je asibiti duba Arfat" "Ashe babban mutum ne ni ban sani ba, ya ce Nabila tana ƙarƙashin kulawar hukuma, saboda rayuwarta na cikin hatsari, wanda take karewa ya rasu, ba a san me zai iya faruwa da ita ba" Kamar shashasha Nasir ya tsaya yana bin su da kallo, shi kuma meya kawo shi cikin wannan lamarin? Tare da Viper suke harƙalla kenan? Amma da kamar wuya ace kamilin mutum da ya san doka, kamar sa ace yana hulɗa da mutumin banza kamar Viper. "Mu'azzam wada kankarofi, mai bawa shugaban ƙasa shawara na musamman a kan harkar tsaro" ya faɗa yana kallon Nasir da ya ga yana yi masa wani irin kallo mai cike da tuhuma". Major ya ce "Haryanzu ina mamaki, da ka ce kai ne dai wada kankarofi, ni na zata suna ne kawai ya zo ɗaya" Alhaji mu'azzam ya ce "A'a, ni ne dai, a rayuwata ina son 'yanci da walwala, dan haka ban fiye son takura ba, ko yawo da gayyar jami'an tsaro ba duk in da zani. Na san ka ɗauki zafi a kan abubuwan da Nabila take aikatawa, na kasada, amma ni burgeni tayi, kuma daga ranar farko da na ganta a law firm ɗin su, nake bibiyarta, nake taimakonta, akwai ire-iren ta, brave citizens, da cin hanci da ƙarfin iko, ya sanya ake tauye su su kasa kataɓus, a kanta na ce bari mu jarraba ayi supporting ɗin ta, mu ga wace irin baiwa da gudunmawa zata bai wa ƙasa, and Alhamdilillah ko iya haka tayi rawar gani " Major ya jinjina kai ya ce "Haka ne sir, amma abun da aka yi ya isa haka, ina son a dawo mini da 'ya ta, abun da tayi Allah ya amfana, ni aikin ma a haƙura da shi, tayi aure. Ba zan lamunci zuba mata ido, tana kare rayuwar ɗan ta'adda ba. Aikinta na neman kawo mini rabuwar kai a cikin iyali. Ga ɗan uwanta yana fafutukar neman mai laifi, ita kuma tana kare shi ba. Sunanta ya ɓaci a idon duniya ba, ina buƙatar ta dawo a haƙura kawai" Alhaji mu'azzam ya ce "Am sorry to say sir, Nabila ta ɗaukko aikin da kammala shi ne kawai mafita, da ceto dubban al'umma, za ta aikata abun da da yawa sun yi yunkurin yi, amma ba su yi nasara ba. Bani da ikon dawo maka da ita, umarni ne na musamman kareta da lafiyar ta" Abba ya numfasa ya ce "Na ji, amma Allah ya amfana haka nan, a dawo mini da 'ya ta, ban ga dalilin da zai sanya, a ɗaukar mini yarinya ba da iznina ba a ɗaga mini hakali har haka ba" Alhaji mu'azzam ya ce "Na san an yi maka laifi, shiyasa muka zo har gida baka haƙuri, kuma ta ɗan samu mini attack ne mun kaita Asibiti, daga baya kuma muka lura da matsanancin haɗarin da rayuwarta take ciki, ka ɗan bamu lokaci" Nasir kamar yayi maganar Viper, amma yayi shiru, kenan da gaske Viper yake shi jami'in sirri ne, ko kuma wata kitumurmurar ce?. Abba suka yi ta jayya da Alhaji mu'zzam, haka ya haƙura, sai dai bai ji zai yi shiru da maganar nan ba, dole a dawo masa da 'yar sa. Bayan tafiyar su, mutanen gidan suja din ga tambayar meyafaru, Abba ya gaya musu ba wani abu, a kan Nabila ne, tana wurin hukuma saboda tsaron lafiyarta. Masu jiran su ji baƙin labari, duk ba haka suka so ba, baba magajiya kuwa addu'a ta cigaba da yi, tare da fatan Allah ya sa Nabila na cikin ƙoshin lafiya. Sumayya ce ta zo gidan, cikin matsananciyar damuwa, ta tarar da Abba yana shirin fita, suka gaisa ya ce "Kin biyo sahu ko sumayya?" "Eh Abba, hankalina ya kasa kwanciya, ni har a radio na sanar a tayamu addu'a bamu ganta ba, na kasa sukuni gaba ɗaya" "Ki kwantar da hankalinki, yanzun nan baƙi suka tafi, wai tana wurin hukuma saboda tsaron lafiyarta, wai wani saurayinta da ya zo dubata kwanaki, wai mai bawa shugaban ƙasa shawara a kan harkar tsaro". Take Sumayya ta gane waye, ta ce "To Abba ya tabattar maka tana lafiya?" "Eh, ya ce suna bata kariya ne, ashe ba saurayin ta bane kawai, ni dai kam na gaji da wannan aikin, ajiye shi zata yi ta fitar da miji, na yi mata aure, ko ni na fitar mata" Sumayya ta ce "A'a Abba ka yi haƙuri, aikin yana da muhimmanci, zan cigaha da kiranta, Allah ya sa na sameta" "Allah ya sa, dan bana tunanin zasu bari ta ɗaga waya". *** Ko da Abdul yayi parking a harabar gidan su, bai ko tsaya rufe motar ba, ya shiga cikin gidan kamar yayi fuka-fukai ya tashi, "Mummy" ya din ga ƙwala wa mahaifiyarsa kira. "Menene wai ka ke kirana haka?" "Ina Daddy?" Ta kalleshi rai a ɓace ta ce "Ya tafi ya gurfana a gaban kwamitin da aka naɗa, na binciken kuɗin da kake neman ka janyo masifa a kansu" "Mummy ba wannan ba, dan girman Allah ki gaya mini idan shi ne ya sa aka je aka ɗauke ramma" Sheƙeƙe ta kalle shi ta ce "Wacece hakan?" "Matata mana" "Wai Abdul baka jin kunyar faɗar wannan maganganun ne? Har wani tutiya kake yi dan ka auri karuwa? Wannan aure da zaka yi alfahari da shi ne, kana wani matarka?" Abdul ya ce "Mummy, meyasa a ƙasashen ƙetare, ko wasu sassan na duniya, idan suka lalata yarinya, ko su gama watsewar su, suke dawowa su aure su, mu kuma sai mu tafka ɓarna mu koma mu ce zamu yi wa Allah wayo, na san ba zan taɓa auren macen kirki ba, dole ragowar wani zan aura, gara wannan ragowata ce koma menene ni na janyo" "Abdul, ka tsaya a gabana ka ke gaya mini wannan maganganun banzan? Ina uwarka" "Ni dai dan girman Allah idan ku kuka ɗauke mini mata, ko dawo mini da ita, wallahi ba zan iya rayuwa mai daɗi babu rahama ba" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ka je kayi duk abin da zaka yi Abdul" "Mummy dan Allah Daddy ne ya saka aka ɗauke mini ita" "Ban sani ba, ka bishi Abujan ka tambaye shi" ta juya ta koma ɗakinta, a matuƙar fusace. **** Wata irin runguma, Ramma ta yi wa mahaifiyarta, suka fashe da kuka baki ɗaya. "Ramma, kina lafiya bai cutar mini da ke ba?" Ramma ta jinjina mata kai tana kuka, suka ƙara ƙanƙame juna. Barrister Habib ya ce "Kukan ya isa haka, a gode wa Allah, dan Allah ku yi wa Nabila Addu'a, da ita da malam garba, shi an bishi an kashe a prison ɗin, amma ita Nabila an kauwwameta, ana tsaron lafiyarta" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, sai da mutumin nan ya rasa ransa?" Maman ramma tayi maganar cikin tashin hankali. Jiki a sanyaye ramma ta ce "Yanzu malam garba ya rasu? Wayyo Allana, Allah ya sa mutuwa hutu ce a gare shi" Suka Amsa da Amin. Mama ta kalli barrister Habib ta ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya saka muku da mafificin alkhairi, idan ka samu ganinta, ka ce mata na gode, na gode Allah ya saka mata da mafificin alkhairi, ya jiƙan magabatanta, yadda ta share mana hawaye, ka da Allah ya bar nata su zuba" Ya ce "Amin, amma ni kuma fa" "Kai ma haka tare da Alhajin da yake ta ɗawainiya da ni" Barrister Habib ya ce "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum, bari zamu cigaba da magana da jami'an tsaron, za a kama ainihin mai laifin, za a hukunta shi da yardar Allah, duk wata shaida muna da ita a kansa" suka din ga yi masa godiya, ya wuce ya fita. Suka ƙara rungume juna, mama ta ce "Lokacin da yarinyar nan take tabattar mini da zata dawo mini da ke, ban zaci da gaske take ba, da zan ganta har ƙasa zan durƙusa na yi mata godiya" Ramma cikin kuka ta ce "Mama ina Sani?" "Mutumin nan da ya saka aka ɗaukkomu, ya kai shi makarantar kwana, ta kuɗi" "Mama wai waye shi? Meyasa ya ɗaukko ki?" "Yana da nasa dalilin, amma ban sani ba" *MONTHS BACK* Nabila sai sauri take yi, takalminta mai tsini yana ƙara, tana neman network, domin yin magana da sumayya, har ta dangana da rukunin ofisoshin da ba kowa a wurin. "Hello, ke Sumayya T ladan, ba network ne, yanzu na samu wuri, ya ake ciki munafukan al'umma" Sumayya ta ce "Nabila ki daina ce mana munafukai, aiki muke fa" "Ba wani aiki, tsegumi wanda aka saka ku, da wanda ba a saka ku ba, duk ku ke samowa ku kwatsawa al'unma komai daɗinsa da ɗacinsa" "Zan ɗura miki ashariya wallahi" Nabila ta ce "Sorry T ladan, masoyiyyar Nabila, bani labari" Da sauri Ramma ta ajiye littafin hannunta, jin an ambaci sumayya T ladan, da sauri ta ƙarasa gaban window tana zura kai. "Baiwar Allah, baiwar Allah kin ganni ta nan baiwar Allah" Nabila ta hau waige-waige, taga ta ina ake magana. "Baiwar Allah wadda take waya, dan ki ƙaraso wurin tagar nan" Cikin dakewa Nabila ta ƙarasa, ta ragar jikin window Nabila ta ga ramma, ta ce "Lafiya kuwa?" Ramma ta ce "Ki taimake ni, kamar yadda Allah ya taimake ki dan Allah, na ji kina faɗar sunan yar jaridar nan, mai aiki a radio" Nabila ta ce "Eh ya aka yi, kin santa ne?" "Ban santa ba, taimakona zaki yi, dan Allah ku sanar da jami'an tsaro idan kuna da dama, wani ne yayi mini fyaɗe, ya sace ni ya aure ni, ba da sanin mahaifiyata ba, ban san a wane halin take ciki ba" "Yayi miki fyaɗe ya sace ki? Garin yaya?" Nan ramma ta gaya mata komai, Nabila ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, kin san irin neman da muke yi miki kuwa? Ni nake shari'a a kan case ɗin ki, har ya fita yana yawo da ke, amma baki yi masa ihu ba, a ƙwace ki?" "Tayaya zan yi masa ihu yana aurena? Kuma idan nayi ihu tamkar na ƙara tonawa kaina asiri ne, wanda ya sanni, da wanda bai sanni ba, sai kowa ya san abin da ya same ni, shi ne mai asibitin nan, shi yayi mini fyaɗe, sai an bi a hankali idan ba haka ba, ba zai taɓa rabuwa da ni ba, dan Allah ki taimaka mini dan Allah, ina son na je na ga mahaifiyata" Nabila ta ce "Tsaya, yana baki ci da sha, ko yana dukanki da cin zarafi?" Ramma ta ce "A'a, baya yi" "Yauwwa Alhamdilillah, a ina yake ɓoye ki?" "Ban san ina ne ba"ta yi maganar tana kuka. Samo abu na rubuta miki lambata, ki faki idonsa, ko saƙo ki turo mini, sai ki goge, nayi miki alƙawarin zaki kuɓuta in sha Allah" Nabila ta bata lambarta, ta nufo hanyar tafiya, tana yi wa Allah godiya, yadda kayanta suka tsinke a gindin kaba, saboda tsananin addu'a da take yi. Daga nan ta koma ƙofar ɗakin Viper, ɗan mama ya hanata shiga. Kamar yadda suka tsara, Ramma ta yi mata message, Abdul na wanka, Nabila ta bawa Viper, ta ce masa wata lamba take so, a duba mata location ɗin ta. Yana dubawa ya ce "Wannan ai lambar ɗan gidan indabo ce" "Waye Indabo?" "Mutumin da ya kashe mini jauhar" Nabila ta rufe baki cikin tsananin mamaki. "A ina ki ka sameta?" Ta ce "Kar ka damu, manta kawai" sai da kanta ya sara, ta ina zata fara yi masa wannan mugun jawabin mara daɗin ji, indabo ya kashe Nura guduma, kuma yanzu ɗansa ya saceta,  bayan yayi mata fyaɗe. Wurin barrister Habib ta je, ta sanar masa da abin da ya faru, sun daɗe suna mamaki, barrister Habib ya ce "Wannan lamarin ba zamu miƙa shi kai tsaye ga 'yan sanda ba, dan bamu san a hannun wa zamu danƙa ba, yana buƙatar sirri sosai da sosai, kar wani yayi mana katsalandan ya ɓata mana aiki". Bayan Nabila ta gano Alhaji mu'azzam, shi ya sama musu wanda suka cigaba da tracking in da ramma take, ta hanyar bibiyar lambar Abdul, har zuwa lokacin da aka yi nasarar gano in da take, jami'an tsaron Civil defense, suka je suka ɗaukkota **** Nabila na tsaye na leƙen window, ta kasa gane a ina take, wurin shi ba jeji ba, shi dai gashi nan. Ta koma ta nemi wuri ta zauna, Viper ya shigo da sallama, ta amsa masa, ya je gabanta ya tsaya, ya ajiye mata ledar abinci ya ce "Gashi nan ki ci ki sha magani" "Vi" "Mmm" "Dan Allah ka mayar da ni gida, ina da abubuwan yi da yawa, yakamata na je ta'aziyyar malam garba, na rarrashi iyalinsa na basu haƙuri, bisa ga gazawata, dama ni ban taɓa shari'a na samu nasara ba, kullum faɗuwa nake yi, bani da sa'a" ta ƙarasa maganar cikin damuwa. "Dama yaushe masifaffen mutum zai yi sa'a?" "Na ji, amma ka mayar da ni gida, ni ban san me ma zan cewa yan gidanmu ba, kwana biyu bana gida, dama ana yi mini iƙirarin bin maza, ban san me zan ce musu ba" Viper ya ce "Na gaya miki, na fisu buƙatar ki, zaki cigaba da zama a nan, har sai kin kammala aikina" "Wai na cigaba da zama kamar yaya? Sai in din ga keɓewa daga ni sai kai, ka san dai bai dace ba, idan mace da namiji suka haɗu na ukunsu shaiɗan ne, ka san bai kamata ba" Ya sunkuyo dai-dai fuskarta, ya tsura nata jajayen idanunsa, da suke razanata wasu lokutan, zaro harshen sa yayi waje, wanda sai da ta tsorata, saboda ganin tsayin harshensa. Ya ɗan ja numfashi ya ce "Lokacin da ki ke sintiri a gidan da nake, kina neman suna, baki yi tunanin na ukunmu shaiɗan bane sai yanzu? Sai dai kece macen kuma shaiɗaniyar, idan zamu shekara dubu, baki isheni kallo ba, wadda take halalina ma, sai da.... Sai kuma ya yi shiru. Ya cigaba da cewa "Kamar yadda na gaya miki, duk wata mace idan ba jauhar ba, namiji ce a idona" "Katako kake gani ba namiji ba" tayi maganar cikin ƙunƙuni. "Ban taɓa ganin abin da ya raina ni ba kamar ke? Amm dama zan gaya miki, ina ganin zan canza lawyer, saboda na lura baki da sa'a ko kaɗan, gashi baki wani goge ba, nafi son wanda zai din ga abin da nake so. Idan na biye miki, sai na koma prison, kuma ƙila nima a bini a kashe a can, kamar yadda aka kashe wannan mutumin, dan haka zan canza lauya". Ɗagowa tayi tana kallon Viper, cikin tsananin mamaki da takaicin abin da yake fitowa daga bakinsa. Fuskarsa a ɗaure, alamar da gaske yake yi. "Bayan duk wannan wahalar da na riga na sha? Ka san zaka ɗauki wani lauyan, amma ka wahalar da ni, nake ta dagewa ina ƙoƙari a kan shari'ar ka na kasa zaune na kasa tsaye?" Viper ya ce "Eh, muddin zaki cigaba da yi mini rashin kunya, tabbas zan sake saka miki ƙarfe wataran, kamar yadda na saka miki da farko, na gaji kin kasa kawo ƙarshen lamarin, kullum sai surutu da shirme ki ka iya" Tamkar ta kwaɗe shi, haka wani abu ya cunkushe mata ƙirji, kawai ta kifa kanta a kan gwiwarta. "Abla, ɗago ki ga" banza tayi masa taƙi ɗagowa. "Kin san magana ɗaya nake yi" ta ɗago idanunta, da suka yi sharkaf da hawaye. Ya ajiye mata takarda a gabanta, takardar umarnin kotu ce, da ta hana kama shi, ɗagowa tayi ta kalleshi, ta rasa ihu zata yi na murna ko kuma me? Kawai ta cukuikuye takardar, ta jefa masa a ƙirji, ta sauka daga kan gadon tana cigaba da kuka" Murmushi ya yi ya tashi ya bi bayanta, cikin kuka ta ce  "Amma a haka kake cewa zaka canza lauya?" Ya ce "Sorry, am just kidding" "A haka ake wasa Vi?, fuska a ɗaure ana zare ido? Tayaya zan gane wasa kake yi?" Tayi maganar tana kuka cike da shagwaɓa. Ya ce "Viper baya manta halacci, ba kuma ya saɓa alƙawari, ko da zaki yi failing sau dubu, ba zan taɓa barin ki ke kaɗai ba, alƙawari ne da na ɗauka" Nabila ta ce "Look at you, i even save your life, amma da haka zaka yi mini albishir da 'yar ƙaramar nasarar da nayi" ya girgiza kai ya ce "Ba ƙaramar nasara ba ce Congratulations, and barrister Habib ya yi miki message, Civil defense sun ɗaukko rahama" a take ta waro ido ta ce "Dan Manzon Allah, da gaske?" Ya jinjina mata kai, alamar eh. Rikicewa tayi, ta durƙusa tayi sujudu shukur, ta tashi, ta shiga kaiwa tana komowa ta ce "Alhamdilillah, ko yanzu na mutu, na cika wani sashe na alƙawarin da nayi, Allah sarki malam Garba, Allah ya yi masa rahama, ni me ma zan yi ne dan daɗi Vi?" Murmushi take yi, tana kuka, tana ta zarya a ɗakin, kamar zata zare, shi kuma sai bin ta yake da ido. Ta je ta tsaya a jikin bango, ta jingina tana sauke numfashi. Ya sake takawa, ya ƙarasa in da take ya saka hannunsa ɗaya ya dafe bango, yana cigaba da tsareta da ido. "Thank you for saving my life 'yar suga" duk da ta takura, amma bai hanata yi masa murmushi ba. Kallonta yake yi, yana tunanin a yaya zata ɗauki ƙaddarar da take bibiye da ita? Ko zata iya jurewa, ko zata gaza kamar yadda yayi? A hankali ya ce "Wannan babbar nasara ce ki ka samu, kamar yadda nayi tsammani, ba kya gori, kamar yadda Jauhar take, na zata da na ce zan canza lauya, zaki yi mini gori, amma ba ki yi ba. Akwai tambayoyi da ki ka yi mini a baya, da wasu wanda nake son na yi miki. Da fari meyasa nayi yinƙurin kashe ki karon farko da na ganki? Meyasa ki ka ga ruɗewa a fuskar liti da walid da suka ganki? Meyasa na din ga korarki idan ki ka zo wurina, nake yi miki barazanar mutuwa? Meyasa su liti suka amince su kawo ki wurina, duk da babu mahalukin da suke bawa damar hakan? Meyasa Indabo ya ke ƙoƙarin yi mini tarko da ke? A yanzu ko a baya, ba za a rasa mutanen da suka nuna miki sanayya ba, alhalin baki san su ba right?" Ta tsare shi da ido tana jiran amsohin tambayoyin. "And as my lawyer, akwai abubuwan da yakamata na sanar da ke, but before then, Abla ni da ke ƙaddara ce mai ƙarfin gaske ta haɗa ni da ke, dan haka dole mu yi haƙuri, mu karɓeta a yadda ta zo mana, saboda pain ɗin da zaki shiga, zai iya fin wanda ni na tsinci kaina a ciki" Tayi tsuru tana kallonsa. Ya zaro wani hoto a aljihunsa, ya miƙa wa Nabila. Hannunta na rawar rashin sanin wace ƙaddarar ce, ta sanya hannu ta karɓi hoton, wata 'yar ƙaramar ƙara ta saki, ta saki hoton a ƙasa, jikinta yana rawa, ta kalleshi ta ce "Soka ke sai na haukace sannan zaka daina yi mini wasa da hankali, menene wannan? Ni bani bace wannan, ni yaushe na sanka har muka yi wannan hoton tare?" Tayi maganar a firgice, tana neman ta raɓa shi ta wuce, amma ya riƙeta a jikin bango, idanunsa suka cika da hawaye ya ce "Matata ce a jiki, ita ce jauhar, 'yar madarata, mace mafi soyuwa a gare ni, matar da ba zan manta halaccinta ga rayuwata ba, matar aljanna da kullum nake fatan na farka daga mummunan mafarkin da nake yi, na farka na ganta a kusa da ni, Nabila meyasa ki ke kama da matata?" Jikinta ne yake wata irin rawa, ta zazzaro ido tana kallon sa. Buɗe ƙofar ɗakin aka yi, suka waiwaya gaba ɗaya suna kallon ƙofar, Alhaji mu'azzam ne ya shigo tare da barrister Habib, da kuma ɗan mama, da yake laɓewa a baya, yana leƙowa. Cikin mamaki Viper yake bin Alhaji mu'azzam da kallo, ba tare da ya saki Nabila ba. Ayshercool 08081012143 78 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa https://whatsapp.com/channel/0029Va9QtrY4dTnBYG1hST2VHADARIN *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* Cak Viper ya tsaya yana bin kankarofi da kallo, zuwa kan ɗan mama da yake ta zazzaro idanu. Kankarofi ya haɗiye wani abu mai ɗaci, saura ƙiris ya yi loosing control ɗin sa, saboda yanayin da ya ga Viper da Nabila. Viper ya a janye hannunsa a hankali, ya tsaya a tsakiyar ɗakin, su kankarofi suka shigo. "Meya kawo ka in da nake?" Yayi maganar a kausashe. "Haba ƙanina, mayar da wuƙar mana, abun rabo ya ƙare, miƙa hannu na menene, bai kamata ace zuwa yanzu muna cigaba da wannan abubuwan ba, ko da ran jauhar, ko babu mallakinka ce, matarka ce dan haka ba zan din ga bibiyarta ba, balle yanzu da babu ranta, ka sassauta wannan kishin dan Allah. Ga Anas, wato ɗan mama yaronka na hannun damanka, da duk wani nasarar aiki da muka yi a kanka, ya faru ne saboda ƙoƙarin sa, sai dai kan mu kai ga bayyana maka komai, ashe ka gano shi, ya gudo wurina hankali a tashe, ya ce na taimake shi, ba zai iya jure hukuncin da zaka yi masa ba, na zo on his behalf, na bayar da haƙuri kuma nayi maka bayanin komai" Viper ya bi ɗan mama da wani irin kallo, ɗan mama ya ce "Na shiga uku, dan girman Allah Oga Viper kayi haƙuri, tursasa mini aka yi, wallahi bani da niyyar cin amanarka, ban taɓa cutar da kai ba, ka san ina yinka, kamar yadda ka ke yi na, kayi mini rai saboda Allah" Alhaji mu'azzam ya ce "Ya isa haka Anas, ni yakamata na wanke ka" duk maganar nan, Viper idonsa na kan ɗan mama, ɗan mama ya sake maƙalewa a bayan Kankarofi ya ce "Gaskiya daga nan kayana zan tattara na gudu Cadi, kallon nan da yake yi mini, tsoro yake bani, bana tunanin zai yafe mini, da ƙyar idan bai saka na gana da Russia ba" Kankarofi ya riƙo hannun ɗan mama, suka ƙarasa gaban Viper, ya numfasa sannan ya ce "Lokacin da uban gidanka yana raye, Dodo, ka fi ni sanin waye shi, ka fini sanin hatsarinsa da imaninsa. Babu wanda ya bawa damar sanin sirrikan da yake da su, kuma ya sani sai kai. Duk da shi ma mai aikata laifi ne, amma yana yi wa hukumomi amfani sosai wurin kama masu laifi, daban-daban. Ya baka horo na musamman, ta yadda yake gane masu laifi, komai kamalarsu, yadda yake iya gane idan akwai kayan laifi a wuri, bai tsaya nan ba ya saka aka baka horo na musamman, a kan fasahar na'ura mai ƙwaƙwalwa. Manyan ƙasar nan na mu'amala da shi sosai da sosai, dan ya san duk wasu hanyoyi da za a iya shiga da fitar da kayan laifi, ciki da wajen ƙasar nan, ba tare da ta an kama kaya ba, sukan haɗa kai da shi, su bashi dukiyoyin su, ya yi musu kasuwancin ƙwayoyi da sauran kayan laifi, ya ruɓanya musu riba a shekara". Viper ya ce "Duk meye amfanin dawo da abin da ya riga ya wuce, abin da na riga na sani, kar ka aibata gawar uban gidana" Kankarofi ya ce "Ba aibata shi nake yi ba, kayi haƙuri na sadaka da gaɓar da nake son na kai ka. Dodo yayi shirin yin murabus, bayan ya koyar da kai manyan abubuwa, da ka iya zama makamin rusa wasu daga cikin manyan hanyoyin aikata laifuka da ba kowa ya sani ba. Daf da zai mutu, ya danƙa amanarka ga manyan mutane da ya yarda da su, ciki har da shugaban hukumar NIA na wancan lokacin, ya basu tabbacin zaka iya basu gudunmawa ta kowane ɓangare, sukaɗai ne hukumar da ya yarda ya damƙa amanarka a hannunsu, duk da kasancewar baka ji, amma kai babban makami ne, ka san manyan sirrukan da bayan shi babu wanda ya sani. Bayan mutuwar dodo, sun buƙaci kaje su baka horo, kayi aiki da su, amma ka ƙi, saboda zuciyarka da tunaninka na kan ɗaukar fansa a kan madaki, kuma rashin yadda ya sanya ka sake cewa ba zaka je ba, dan baka da tabbacin ta wace hanya zasu yi amfani da kai. Bayan aurenka da jauhar, bayan na shiga damuwar rashinta, wataran muna hira da cousin ɗina, wanda shi ne aka danƙa amanarka a wurinsa, muna hira, yake bani labarinka, a nan na gano cewa lallai kai ne ake magana a kai, na cigaba da matsa masa, a kan lallai suyi ƙoƙarin su ga sun ɗauke ka, zaka yi musu amfani sosai, a lokacin ina fatan silar aikin, ka daina wani abun, kuma ka samu hanyar kula da Matarka. Har bincike na saka aka kuma yi mini sosai a kanka, a nan na gano kana aiki da Indabo, abin ya ɗaure mini kai ya bani mamaki. Bayan wani lokaci, ban san meyafaru ba, na samu labarin ka je ka basu haɗin kai, an kama ɗan gidan indabo a Mexico, da laifin safarar cocaine, duk da babu wanda ya sani, amma ni ina da hanyar samun bayanai na a kanka. Na cigaba da fatan Allah yasa daga haka su hilace ka, ka amince da aikin nan, amma sam baka da intrest a kan haka. Wasu lokutan Hafsa kan bani labarin, irin soyayya da ƙaunar da ka ke yi wa jauhar. Kwatsam na samu labarin mutuwar ta, wai ka sha miyagun ƙwayoyi ka kasheta, sai dai sam ban ji na yarda ba. Daga yadda na bibiyi case ɗin silently, naga sam babu adalci, a yadda aka gudanar da binciken da gurfanar da kai ɗin ma a gaban kotu, kuma na samu labarin abokin gabarka, Madaki shi ya maye gurbin aikinka, a wurin Indabo. Ni na saka aka kamo Anas ɗan mama, aka matsa mini shi, yadda yakamata kasancewar sa, yana cikin tsagerun dabar Madaki. Shi ya tabattar mana da Madaki ne ya karɓi kwangilar kasheka a wurin Indabo, amma azal ɗin ta hau kan matarka. A lokacin shugaban ƙasa ya samu nasara a tenure farko, kuma yayi mini S.A ɗin sa na fannin tsaro, haka zalika ya tafi da ɗan uwana a matsayin shugaban hukumar NIA. Sosai nake biyan ɗan mama, ya koma wurin su Walid, tun suna korarsa, suna hantararsa, har suka saki jiki da shi a dabar su, duk da kasancewarsa yaron madaki, suka bashi cikakkiyar kariya daga Madaki, yana reporting duk wani motsinka a gareni, da kuma hukumar NIA, hakazalika ni ne nake tura maka saƙonni. Tabbas nayi amfani da kai dan cimma nawa muradin a kan indabo, kuma taimakonka nayi, sauran abin da ya faru ka sani, ni nake sanya a goge duk wani sahun laifi daka aikata, ta hanyar amfani da jami'an Civil defense, kan daga baya, hukumarku ta karɓi ragamar cigaba da kula da kai, tare da turo maka gayattar dawowa ka cigaba da aiki da su ta hanyar ɗan mama, da yake ajiye maka rigunan aiki, ina nema masa afuwa, shi ma umarni aka ba shi da dole ya bi" Viper ya din ga haɗiyar wani yawu mai zafi, yana son yayi magana, Nabila ta dafe kanta ta ce "Wannan wane irin abu ne wai, gaba ɗaya sai juya mini kaina ake yi, na kasa gane komai, wai menene haka" tayi maganar cikin ɗaga murya, tana dafe kanta. Viper ya juya ya koma in da take, ya durƙusa ya ɗauki hoton Jauhar da yake ƙasa, kawai Nabila ta tafi zata faɗi, idanunta a lumshe, ya riƙe ta, amma ya kasa magana,a hankali ya ja ta, ya mayar da ita kan gadonta. Ta ce "Bana gani, duhu nake gani, kaina zai fashe" kankarofi ya nufo gadon, amma Viper ya ɗaga masa hannu, ya ce "Excuse us please" Kankarofi ya tsaya yana kallon Viper, Viper ma ya ƙura masa ido. Barrister Habib ya ce "Ina son zan yi magana da ita" Viper ya ce "Ka jira tukuna" Kankarofi yayi musu alama, da su fita, haka duk suka fice. Nabila ta dafe kanta, ta cigaba da kuka, ya ce "Wai kukan me ki ke yi haka?" "Ni ka rabu da ni dan Allah, ka ƙyale ni, so ka ke na haukace, gaba ɗaya kun ruɗa mini kai, sai ƙara bijiro da wasu abubuwa ku ke yi da ban san da su ba, ni ka rabu da ni". "Ki tsaya ki saurare ni" "Ba zan saurareka ɗin ba, ba na son jin komai, ni ka rabu da ni" "Am talking and you are misbehaving" yayi maganar cikin tsawa. A razane ta dafe kanta, ta faɗo daga kan gadon, ta takure a wuri guda tana kuka. Ya tashi ya sake dawowa gabanta, amma ta hau jifansa, da abun da duk ta samu a kusa da ita. Shiru yayi yana kallonta, yana tuna lokacin da jauhar ta burkice masa, da yayi mata laifi, ta din ga jifansa da kwanuka, yayi ajiyar zuciya ya kira wayar Asibiti. Mintuna kaɗan likita ya shigo, ya tarar da Nabila kamar mai shirin zarewa, ya yi mata magana, amma tayi masa shiru. Ya fita ya dawo da allura, ya kama damtsenta zai yi mata, taƙi tsayawa, sai da Viper ya riƙeta aka yi mata, sannan jikinta ya saki ta hau lumshe ido. "Viper, garin yaya ta zama haka lokaci guda? Ba ta fara samun sauƙi ba?" Viper ya ce "Ta ɗan samu damuwa ne, idan ta farfaɗo ta samu sauƙi, kawai a sallame mu" Likitan da yake sanye da wandon sojoji ya ce "Viper, discharge kuma? Why? Ba haka aka shirya ba, tana ƙarƙashin kulawar hukuma, kai fa shegen taurin kai ne da kai, sai ka janyo wata matsalar tukuna?" Viper ya ce "She's not safe here, zamu bar wurin nan" "Zuwa ina kuma? Akwai wanda zai shigo cikin barrack, ya zo asibiti yayi mata wani abu ne?" "John, i want her to be discharged" John ya ce "Ko nayi discharging ɗin ta, ka san ba zata bar wurin nan ba, sai an bamu izinin hakan. Let me help you put her to bed, she's already sleeping on the floor" wani irin mugun kallo Viper ya yi masa, ya ce "Ohh sorry" ya juya ya fice. Viper ya sunkuya yana kallonta, fuskarta ta koma ja, sai tsatstsafar da gumi take yi, da gani baccin na dole ne kawai saboda allurar da aka yi mata. Zai iya cewa ya bai taɓa ganin mace mai naci, da tsantsar jarumta, kamar Nabila ba. Duk da baya son taɓa ta da yake yi, amma dolensa ya ɗagata ya mayar da ita kan gadon, ya gyara mata kan gadon, ya juya ya fito. A waje ya tarar da Alhaji mu'zzam da barrister Habib, da ɗan mama a zazzaune. Ya taka ya ƙarasa gaban Alhaji mu'azzam, ya ce "Meyasa ka zaɓi irin wannan lokacin, ka gaya mini wannan maganganun a gabanta? Na gaya maka ni zan kawo ƙarshen wannan lamarin, tun da ni ya shafa, abu ne mai nauyin gaske da ɗaukarsa ba lallai ya zama abu mai sauƙi a gareta ba. Dan haka bana buƙatar ka a cikin abin da ya shafeni ya shafi abin da ya shafe ni. Wadda ta haɗa ba rabonka ba ce ba, ban san dalilin da zai sanya ka din ga bibiyar rayuwata ba kamar kana bi na bashi ba" "Muddin za a bayar da labarin jauhar, dole mu'azzam zai fito a ciki, ban cigaba da bibiyarka dan ina neman wani abu a wurinka ba, na bibiyeka na taimake ka ne, domin mu taimakawa juna, daga ni har kai, buƙatata ta biya kaima taka haka, naga bayan indabo, kai kuma ka ɗauki fansar tozarci da zaluncin da aka yi maka. Ban da ƙaddara ta Ubangiji, na rigaka ganin jauhar, kuma aurenta nayi niyyar yi, amma Allah ya nufa matarka ce, na so jauhar so na haƙiƙa, amma na kawar da kai, duk na shiga tashin hankali jin irin mutumin da ta aura, yanayin zamanku daga baya ya sanya na samu kwanciyar hankali, kisanta da abin da aka yi maka ya bani ya sanya na tausaya muku nake bibiyarka. Nabila ma na rigaka ganinta, ni ba a garin kano na fara ganinta ba, tun a Abuja wurin da aka basu rantsuwar zama cikakkun lauyoyi. Sai da na kusa rasa hankalina da tunanina, saboda tsananin tashin hankali da ruɗewa, har sai da na zata ko matsalar ƙwaƙwalwa na samu, saboda damuwar kisan gillan da aka yi wa jauhar. A lokacin ban yi ƙasa a gwiwa ba, na tashi yin bincike a kanta, har zuwa wannan lokaci, nake bibiyarku daga kai har ita. Muddin ba butulci zaka yi mini ba, na taimakeka Aminu, ko nayi maka laifi a wani wurin, wani wurin na taimake ka". Sai da ya gama tsaf Viper ya ce "Na nemi taimakonka ne? Wane irin taimako ne kayi mini kana yawo da hankalina, ka yi mini shi a munafunce? Ka din ga wasa da hankalina kana ɓoye kanka? Madalla da abin da ka yi, amma ina buƙatar abin da ka ke yi ya tsaya a iya nan, Nabila da abin da ya shafi rayuwar ta hurumina ne, daga nan idan ta farfaɗo zan bar wurin nan da ita" "Waye ya baka wannan damar? A ƙarƙashin kulawata take ba taka ba, naje na samu mahaifinta ma, na sanar masa da hakan, sai dai kai ka bar nan wurin, amma Nabila na tare da mu" "Don't cross the boundaries! Ban ƙi ayi mutuwar kasko ba, ba na wasa da duk abin da ya shafi marigayyiya, a kanta ba abin da ba zan aikata ba, idan da na koma na ɗauki wannan rigar ce, zan cireta na ajiye, kar ka sake kusanto in da nake, bana buƙatar taimakonka" Kankarofi ya ce "Jauhar ce mallakinka, Wannan kuma Nabila ce" "Na gaya maka Nabila ta haramta ga kowa muddin ina ganin fuskar matata a jikinta" Viper ya yi maganar yana zazzaro ido cikin matsanancin kishi, jijiyoyin kansa suka ɗaɗɗaga. Cikin hanzari ɗan mama ya fito, ya shiga tsakanin Kankarofi da Viper, barrister Habib gefe ya koma, dan gaba ɗaya Viper tsoro yake bashi. Hankalin sojojin wurin ne, ya fara dawowa kansu, suka tattaso suka nufo su, Viper sai huci yake yi. "Easy oga, ka fahimci al'amarin nan dan Allah, wallahi Yallaɓai mai ƙaunarka ne, ba ya nufin cutar da kai, ba ƙaramin taimako ya yi maka b..... "Shut up! Da na ƙyaleka ban ce maka komai ba, ka ke gaya mini maganar banza, ka kuma yi mini magana, sai na tatsule ka a wurin nan, menene na cigaba da bibiyar rayuwata dan na auri wadda ya so ya aura, menene amfanin haka?" "Wadda ake yi domin ta, ta bar duniya, ba shi da wata mummunar manufa a kanka, ka fahimci hakan oga dan Allah" Ya nuna ɗan mama da yatsansa, alamar kashedi. "Viper wai me ka ke yi haka ne? Oga ne fa da kansa a wurin nan, ka ke ɗaga masa murya ka ke faɗar maganganu" Viper ya ce "Bana buƙatar sa a rayuwata, ya bar wurin nan, ko kuma ni yanzu na bari" Ɗan mama ya koma wurin kankarofi ya ce "Dan girman Allah sir kayi haƙuri, wallahi Viper yana da kirki, kar ka ce zaka cire hannunka, tsabar kishi ne kawai, kar ka ce sai ka na son Nabila sai ka aureta" Kankarofi ya ce "Yaron ba shi da kunya, ba kuma shi da ɗa'a, ban yi zaton haka daga gare shi ba" Ɗan mama ya ce "Wallahi Viper yana da ɗa'a da biyayya, kawai ka san soyyaya ba ta da gwani ko jarumi, na san dai yana da taurin kai da azabar fushi, amma wallahi duk faɗansa yana da kirki, kar ka manta, da shi nake kwana nake tashi muke rayuwa. Amma ba haka yake ba, dan Allah kar ka cire hannunka a kansa, zan yi maka proving abin da na gaya maka, ai na san maganinsa, zai nustu bari ya gama hargowar". Ana ta fama da Viper, ya ce sai ya bar Asibitin da Nabila. Liti ne ya ɗaga wayar Walid, ganin kiran ɗan mama ne ya ce "Kai dan ubanka, ina ka shiga kwana biyu baka nan, baka sanar mana ina ka tafi ba, Viper duk ya addabe mu, ko wani rashin gaskiya ka fara ne?" Ɗan mama ya ce "A'a oga liti, akwai matsala ne, ina oga walid?" "Yana banɗaki matsalar me? Tsokana ka yi ko me? Kana ina ne?" "Ina cikin barikin sojoji" Liti ya ce "Iyee, ba wurin yan sanda ba sojoji? Ɗan mama me da me ka ke sha ne? Sojoji fa ka ce? Me ka yi musu?" "Dan Allah ku zo, da kai da Oga walid, ku kaɗai ne zaku yi solving case ɗin nan" Liti ya ce "Kai, duk iskancina, ban taɓa tsokanar wannan mutanen ba, da babu Allah a ransu, haka kurum su tumurmusa ni a banza, su sauya mini kamanni, Allah ya ƙwatoka, bari Walid ya fito ko zai iya ƙwatoka, dama ya fi ni imani da tausayi, ko shi ko Viper, dama shi ya saba da jure wahala. Dukanka suka yi ko kuma karairayaka suka yi?" Ɗan mama ya ce "Ba ɗaya, matsala aka samu ne" "To Allah ya yi maka maganinta, ya tsayar iya kanka, Allah ya sa idan su Walid ɗin sun zo su ganeka, ba su sauya maka fasali ba, su mayar da kai gorilla ko wata halittar ba" Walid ya ƙaraso, ya karɓi wayar daga hannun liti cikin tashin hankali ya ce "Ɗan mama, kana ina ne? Meyafaru meya kai ka wurin sojoji ne?" "Oga walid, lafiya ƙalau fa, wani case ake yi, ina tare da oga Viper, ku yi sauri ku zo dan Allah, kar ya aikata wata ɓarnar, ku kaɗai ne zaku iya shawo kansa" Walid ya ce "Kai da Viper kuma a cikin barikin Sojoji? Garin yaya?" Liti ya miƙe ya ce "Viper kuma? Ka gani ko? Viper wasu lokutan baya lissafi ko shawara, kawai ya ɗibi jiki ya tafi, Allah kaɗai ya san me ɗan maman yayi musu, ya janyo an kama shi" Walid ya katse wayar ya ce "Muje dai mu ji menene, ka san babu yadda za ayi Viper ya bar ɗan mama ko wa ya tsokana kuwa" Liti ya ce "Ai da yake ba mutunci ne da shi ba, kwana nawa muna nemansa, da ya tafka tsiyarsa kai tsaye kuma sai ya nemi Viper ba mu ba" haka suka tafi, liti yana ta masifa. Al'amin na ɗakin da Nabila take, shikaɗai ya kasa ya tsare, ya zuba mata ido, tana ta bacci. Tun da aka yi wannan dambarwar yaƙi fita, gani yake yana matsawa zasu ɗauke Nabila. Ji yayi an buɗe ƙofa, ya waiwaya. Wasu manyan sojoji suka shigo, ɗaya ya ce "Viper, taso muje ko" "Muje ina? Am not going anywhere" "Meyasa ka ke haka ne, kar ka saka mu yi faɗa da kai fa" Viper ya ce "Wace azaba ce ni ba a gana mini ba, ba zan je ko ina ba, ban san me kuka haɗa kai da mutumin nan, ku yi mana ba" da ƙyar suka lallaɓa shi, suka fita zuwa wani sashe na barrack ɗin. Suna shiga wurin, ya ga liti da Walid, sai dai still ya ga kankarofi, take ransa ya kuma ɓaci, yana mamakin taurin kai da rashin zuciya irin na kankarofi. "Me kuma zan yi maka? Me kake so kuma yanzu?" Walid ya miƙe ya ce "Mai zamani" Viper ya ɗaga masa hannu ya ce "Mai laya" Walid ya ƙarasa gaban Viper ya ce "Mai zamani, easy mana cool your temper" yayi maganar yana ɗan dukan ƙirjin Viper. "Meyasa yake bibiyata, dan na auri matar da ya so aura?" Yayi maganar cikin damuwa. "Ta rasu fa yake bibiyarka, da tana raye ya bibiyeka ne?" Viper ya yi shiru. Walid ya ce "Kishi ne yake damunka, an fara yi mana bayani, bawan Allah nan, ya taimaki rayuwar ka ta fuskoki daban-daban, ka nutsu ka kwantar da hankalinka, mu taimaki rayuwar Nabila. Ba zai yiwu ta cigaba da zama a nan ba, tun da Asibiti ne, kayi haƙuri a samu kauwammanen wuri a ajiye ta, idan ya so kaima ya zamana kana tare da ita. Wancan abokin aikinta ne, kuna buƙatar ƙawarta 'yar jarida, da sauran su, kai a tunaninka effort ɗin ta kawai ya isa ya sanya ku yi Wannan nasarar? A Nigeria fa muke, dole sai da wa ka sani wa ya sanka, ka danne koma me kake ji, mu fuskanci gaskiya. Butulci da manta alkhairi ba halinka bane mutumina, ka ajiye kishi a gefe, muna buƙatar a bi mana hakkin jauhar, muna buƙatar yi wa Nabila tukuici da abu mai muhimmanci, idan ka ɓata aikin nan saboda taurin kai, ba ka yi musu adalci ba, ciki har da ita da mu kanmu da muke tare da kai" Viper ya ja jiki ya zauna a hankali. Liti ya ce "Ɗan mama duk zaman da muka yi da kai, ashe aikin munafunci ka ke yi, amma kuwa ka yi asara dan wannan ba aikin yi bane ba, kuma saboda tsabar ƙwarewa, ko da wasa baka taɓa gaya mana ba. Ni dama na daɗe ina zargin baka da gaskiya" **** Miƙa tayi sosai tana addu'a, ta ji kamar gadon da take kai, ya sha bamban da wanda ta kwanta a kai, ta tashi zaune a hankali, ta ganta a cikin wani katafaren bedroom, bisa wani ƙaton gado. Tayi tsuru da ido, tana tunanin ko mutuwa tayi. Wata mata ce tayi sallama, ta ce "Kin tashi? Ga banɗaki nan idan zaki yi alwala ki yi wanka ki rama sallolin da ake binki". Nabila ta ce "Ina ne nan baiwar Allah? Ko mutuwa nayi ne?" Matar ta ce "A'a, wanda suka kawo ki, zasu zo su yi miki bayani, ga kaya nan ko zaki canza". Ta tashi a hankali tana addu'a, ta shiga banɗakin, ta yi wanka, ta yi alwala, ta fito ta din ga salloli, daga iya abin da ta iya tunawa, ga wata irin yunwa tana ji, gaba ɗaya ta kasa tantance meyake faruwa gaba ɗaya. Matar ta dawo, ta kawo mata abinci, amma Nabila ba ta taɓa ba, ta takure a gefe. Viper ne ya shigo, ta ɗago kai ta ƙura masa ido, har ya ƙarasa gabanta, ya zauna ya ce "Sannu, ya jikin?" Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Kamar nayi kuskuren yinƙurin taimaka wa rayuwarka, kana ƙoƙarin rusa tawa, ta hanyar ganin ka haukata ni, me nayi maka haka? Kuma ina ka kawo ni nan?" "Ba ki yi kuskure ba, domin kuwa kin yi sara ne a kan gaɓa, kuma zaki alfahari da ƙaddarar da ta haɗa ni da ke" "In yi alfahari bayan na haukace ko?" Viper ya girgiza kai ya ce "Ba zaki haukace ba, tambayoyin da nayi miki, haryanzu nima ina buƙatar samun amsarki, sai dai bani da tabbacin samun amsarsu duka. Amma bari mu gani, ko a cikin abin da zan gaya miki zamu gano bakin zaren, rayuwata kamar ƙwallon ƙafa take, daga wannan ƙafa zuwa wancan, daga wannan tudu zuwa wancan rami. A haƙiƙanin gaskiya, ban yi shekaru biyar a gidan yari ba". Nabila ta waro ido tana kallonsa. "Nayi zaman gidan yari, cikin tsananin razani, cikin matsananciyar damuwa da ƙuncin zuciya, tare da fatan Allah ya sa da an mayar da ni kotu, a yanke mini hukuncin kisa, na huta, amma ranar da aka saka a cigaba da shari'ar ta wuce ba a cigaba ba. Azaba da wahalar da nake sha a gidan, bai ɗaga mini hankali ba, kamar yadda halin da nake ciki, bai hana wasu din ga ƙoƙarin nemana da mummunar ɗabi'a ta neman maza ba, ciki har da ma'aikatan wurin. Abin da su madaki suka yi amfani da shi suka shaƙa mini, ya cigaba da affecting ɗina. Azaba da takura, ya sa na zame musu mahaukaci, na danne wanda suke cewa sarkin gida, na kusa janyo maƙogwaronsa waje, nayi masa dukan mutuwa, saboda sun zata dolo ne ni, duk da sun san labarin waye ni, prsion ɗin ta sha banban da wadda ake kaini. Suka ajiyeni a wani wuri, suka din ga gana mini azaba, wai nayi yinƙurin yin kisan kai, ba wanda ya duba abin da ya neme ni da shi. Aka ajiyeni, babu wanka, babu wanki, babu ci babu sha, sai azabar duka. Wurin ga ƙazanta da rashin tsabta, a haka kuma a kan fito da ni, ace za a saka ni aikin wahala. A halin da nake ciki, na tsinci wani ɗan ƙarfe, da zai iya zama makami, na farwa wani, dan fuskar madaki na gani, sai da aka ƙwace shi da kyar, na huda masa wuya, sannan naga ashe ba shi bane ba, ƙwaƙwalwa ta ce ta fara samun matsala, banda kururuwar da nake yi wasu lokutan, ina kiran matata da ɗa na, tare da alwashin kashe madaki. Aka rabani da sauran fursunoni, aka ce na haukace. Watarana, cikin dare ina kwance, na san idona biyu, amma bakomai nake ganewa ba, fatana na farka daga baccin da nake yi, na ganni tare da matata. Kawai wani mutum ya saka mukulli ya buɗe in da nake, ya fara lalubena, duk a galabaice nake, kwana uku ba abin da aka bani na ci, sai na tsaya naga me zai yi mini, kar nayi masa wani abun, na je ƙwaƙwalwata ce take gaya mini shirme, kamar yadda ta saba. Sai na ji bai nufi yi mini lalata ba, kawai ya soka mini wani abu, kamar allura a cinyata, ya fara zuba mini wani abu mai tsananin zafi a jikina, ruwan allurar na shiga, ina jin kamar ana fizgar naman jikina, a take na kurma ihu, na tashi na shaƙe shi, ina dukansa, ina cewa shi ya kashe jauhar, sai na kashe shi. Ina dukansa jikina yana ƙara sanyi, kamar ana zare mini laka. Aka zo aka raba ni da shi, nayi masa jina-jina, ni kuma na faɗi a wurin, basu bi ta kaina ba, suka fice da wancan. Ina kwance na ji wani abu mai sanyi na bin hancina, a taƙaice dai, kasheni yayi yinƙurin yi mutumin. Washegari ina kwance kamar gawa, ina jin duk abin da ake yi, amma ba zan iya motsi ko magana ba, aka ɗauke ni, aka ce za a kai ni Asibiti, ayi mini magani, ashe wasa farin girki, maimakon a kaini asibiti, sai aka yi wani wurin da ni....... Ayshercool 08081012143 79 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* "Bana iya gane ina ake, saboda a matuƙar galabaice nake, amma naji a jikina, yakamata ace idan asibiti ne ya ci ace an je, duk da bana sanya ran zan rayu, a maganar da mutanen motar suke yi, jini nake ta fitarwa ta hancinca, ga azabar yunwa da datti, na gidan yari, tufafina tamkar mahaukaci, dan a mazaunin da aka ajiyeni kenan. Aka yi parking ɗin motar, aka canza mini wata, wadda nake kyautata zaton ambulance ce, dan a ciki aka toshe hancina da bandeji, saboda jinin da nake zubarwa, aka saka mini ruwa, muka cigaba da tafiya. Tun ina jin maganganun da ake yi a motar, tafiya taƙi ci taƙi cinyewa, har na daina gane komai, na buɗe ido na ganni a wani wuri, a kan gadon asibiti, an tuɓe kayan jikina, sai gajeren wando, na tashi a gigice cikin matsananciyar kiɗima, ina ihu saboda ban san meyafaru da ni ba, na farka ina zaton zan ga madaki da jauhar, ina hana shi cutar da ita, wani ɓangaren ina tunanin ko ina prison ne, wani yayi galaba a kaina. Sai dai na ji ni a ɗaure da ankwa dukka hannayena, na din ga ihu saboda yadda naman jikina yake yi mini wani irin azababben zugi, kamar ba zan rayu ba. Wasu mutane da ban san suwaye ba, suka zo kaina, da allurai suka yi mini, ɗaya daga cikin su ya ce "A cigaba da kula da shi mu gani, will he survive the poison, duk yadda zaku yi, ku yi ƙoƙarin ceton rayuwar sa" haka na sake fita hayyacina na farka, sai dai a wannan karon, ban ji wannan raɗaɗin ba. Aka cire mini ankwa, aka tashe ni zaune, aka kawo mini abinci, kamar mayunwacin kare, haka na dirarwa abincin nan, kamar zan haɗa da kwanon saboda yunwa, ina ci ina jin kamar ana yayyanaka kayan cikina da wuƙa, amma azabar yunwar da nake ji, ya sanya naƙi daina ci, sai dai ban gama ci ba na din ga amai, haɗe da jini, wai duk cikin side effect ɗin allura da aka yi mini ne, kashe ni aka so ayi. Ba a sake bani abinci ba, sai ƙarin ruwa da allurai, mutanen wurin ba kowa ke jin hausa ba, ni kuma bana magana, suna bani damar yin salla, aka fara koya mini cin abinci. Ba wanda na tambaya dalilin kai ni wurin nan, kuma babu wanda yayi mini bayani, a haka har na shafe wata guda cif. Duk yadda suka so nayi magana, bana yi, sai dai wasu lokutan ina rasa tunanina, na din ga ganin madaki da jauhar a zahiri, na din ga yinƙurin shaƙe duk wanda yake kusa da ni. Sai da na ɗan samu nutsuwa, aka aske mini gemuna da sumar kaina gaba ɗaya, aka kuma saka mini ankwa, aka rufe mini ido, aka sakani a mota, aka bar wurin da ni. Wani wurin aka sake kai ni, mu huɗu ne a wurin, kowa da wurin da ake ajiye shi tamkar ceil. Na fauskanci nikaɗai ne musulmi babu bahaushe, sai ƙabilu, kullum bayan nayi sallar asuba, da sassafe haka za a kaimu wani wuri, ana bamu training na azabatarwa, wanda ka iya zama ajalin mutum. Idan muka gama, zamu saka wasu riguna, masu tambarin dragon, za a kaimu wani wuri, in da ake bamu darasi, malamanmu turawa ne, class ɗin mu huɗun nan ne, kowa da computer sa, ayi mana darasi ta online. Waɗanda suke kula da mu, wasu irin zaratan ƙartin sojoji ne, sun kai su goma sha biyu, a kan mu huɗu kawai. Azaba ta ishe ni, ban ga alamar za a mayar da ni gida ba, na gaji, gaba ɗaya na rasa ina rayuwata ta dosa, bani da wani burin da ya wuce na mutu na huta. Za a bamu abinci mai kyau, a bamu abin sha mai kyau, amma azabar da ake mana ta ishe ni. Wataran ana tsaka da bamu training, na fizgi bindigar wani, nayi yinƙurin kashe kaina, suka riƙe ni, aka ɗauke ni aka kai ni wani ɗaki, da ban zaci zan fito da rai ba. Sai da na kwana bakwai a ɗakin, ko class bana zuwa. Ranar na takwas, ogansu ya zo ya same ni, yake tambayata meye matsalata na yi yinƙurin kashe kaina. Na ce masa su mayar da ni garinmu, ina son ganin matata. Ya ce mini muddin ina son komawa gida, sai na basu haɗin kai, na yi wa ƙasata aiki, sun san ni yaron dodo ne, kuma akwai amfanin da zan yi musu, dan haka dole na mayar da hankali a kan training da kuma karatun da nake yi, kuɗi aka ware masu nauyi, saboda mu yi wannan karatun. Na ce ni ba zan yi ba, su kasheni kawai su daina wahalar da rayuwata. Ya ce ba zasu kashe ni ba, in yi abin da suka umarceni, idan ina son na ga matata. Sai na tambaye shi, matata na raye? Ya ce tana raye, zan ganta idan na daina taurin kai, nayi abin da ake so. Kuma ko ina so ko bana so, ubangidana ne ya nema mini wannan aikin, tun kan ya mutu, dan haka sai dai na mutu a process ɗin, tun da na san sirruka masu muhimmanci da zasu taimaki ƙasa. Na din ga tunanin, wane irin laifi na yi wa dodo, zai zaɓa mini wannan azabar, sai dai tsananin ɗoki, da daɗin bakin zan ga matata, ya sanya na saduda, gashi suka saka mini ido sosai da sosai, saboda suna iƙirarin bani da lafiyar ƙwaƙwalwa, kuma bana ji. Wata makaranta muke yi a russia, ilimin na'ura mai ƙwaƙwalwa kawai ake bamu, duk da na san abubuwa da yawa ni, ta online muke makarantar, a training ɗin nan aka koya mana duk wani nau'i na haɗawa da wargaza bindiga, ilimin makamai, leƙen asiri, da duk wani nau'i na abin da ya shafi harkar tsaro. Suka ce mini ƙwazona, shi zai bayar da damar komawata garinmu, har naga matata, na roƙe su ko a waya, a haɗani da matata tun da sun ce tana raye, suka ce ba zasu haɗamu ba, zan ɓata musu aiki. Na zage damtse, lokutan jarrabawa, ina cikin overollers, ina tashi da points masu kyau, na fara sabawa da wahalar training, jikina duk ya murɗe, sai dai babbar matsalata bana cikakken bacci, bana iya bacci, da na rufe idona, zan ganni a falo, tare da jauhar madaki zai kasheta, gaba ɗaya sai na tubure musu, na hau ihu. Ko abincin da nake ci, bana cin sa ta daɗin rai, saboda damuwa da tunani. Abokan karatuna a kan basu damar shan giya, har mata a kan kawo musu, amma ni duk ba wannan a gabana. Tun ina lissafi da sanya ran ƙarewar wannan wahala, naga babu rana babu wata, na zauna nayi tunani, babu yadda za ayi, jauhar na raye a gurfanar da ni a gaban kotu, a tuhume ni da laifin kisan kai, naga kawai raina mini hankali suke yi, sai kuma wata zuciyar ta ce mini ai mafarki nake yi, sai dai na rasa wanne ne mafarkin wanne ne zahirin?. A haka na shafe shekaru a wurin nan, ban taɓa barin kewayen in da muke ba, na rayu da matsanancin ƙunci da damuwa a zuciyata, wasu lokutan sai an yi mini allurar bacci nake iyawa. A haka muka kammala karatu, sauran ukun aka ce, za ayi posting ɗin su, in da ake son su gabatar da ayyukansu, ni kuma sai an yi settling issue ɗina. Mun zama sojojin leƙen asiri. Ni dai jinsu kawai na din ga yi, sauran suka din ga murna, aka shirya mana walima, sauran duk sun saba da su, ni duk yadda aka so ja na a jiki, a yi raha da ni, a saba ban yadda ba, dan ni kaina na san rabi mai hankali rabi mahaukaci nake. Abokan karatuna kuwa, basa shiga harkata, dan duk lokacin da ƙwaƙwalwa ta ta haska mini fuskar madaki, a jikin ɗaya, sai na kusa kashe shi, dan duk da training ɗin da aka bamu, na fi su ƙarfi nesa ba kusa ba, kuma ba addinmu ɗaya ba, ba ƙabilarmu ɗaya ba. Sai da na ji haushin dodo, duk da baya raye, na ji ya sakani a masifa, duk da ina fatan sanya indabo, biyan bashin abin da ya aikata ciki har da kisan dodo. Ana gobe za a mayar da ni kano, ina ta murna zan koma naga jauhar, naga ɗana, dan na san a lokacin ya yi wayo, ban san meyafaru ba, ko me suka yi mini ba, sai farkawa nayi, na ganni a prison. Hakan ya ƙara burkita ƙwaƙwalwa ta, na fara tunanin wani mafarkin na kuma yi, na din ga kiran sunayen shugabbaninmu da suka bamu training, ina cewa su zo su cika mini alƙawarin da suka yi mini, su haɗa ni da jauhar ɗina da ɗana kamar yadda suka yi mini alƙawari, gashi ko za a kashe ni, ban san sunan garin da aka kaini ba. Gandirobobi, suka yi mini dukan tsiya, wai na cika musu kunne da hauka, matar da na kashe da hannuna, bayan na sha na bugu, na amsa hakan a kotu, yanzu kuma na zo na ishe su da shirme. Suka yi mini dukan tsiya, amma na kasa daina kururuwar kiran sunaye da magiyar su haɗani da jauhar, gaba ɗaya na zama mahaukaci, ni kaina a lokacin na yadda ni mahaukaci ne. Wasu lokutan idan na buɗe jikina, ina ganin tabon raunuka da wahalar da na sha a wancan garin, amma fafur aka nuna hauka nake yi, da sambatun ƙarya. Tun da suka tabattar mini ni na kashe jauhar, na ƙara rasa tunanina, damuwa da tashin hankali suka koma sabbi fil. Kusan watanni uku, cikin dare ina kwance, dama ɗakina daban, aka tashe ni aka ce na fito, na fita na bi bayan wanda suka kira ni, aka fitar da ni wajen gate, wai an karɓi court order na tafi. Na tsaya ina kallonsu, ina mamakin wane mafarkin kuma na sake shigowa, suka rufe gate ɗin prsion ɗin, suka bar ni a tsaye. Zuciyata ta raya mini maza kafin na farka daga baccin, na je na ga jauhar, ko zan farka dai na ganta. Na fara tafiya a duhun nan, har garin Allah ya waye. rana ta ɗaga, na isa unguwar mu, ban manta hanya ba. Sai dai Abbu ya tabattar mini da jauhar ta mutu, ni na kasheta, na tafi na bar masa gida. Mutanen unguwa suka din ga kallona, har da masu gudu. Babu tunanin komai ko tsoro, bayan na je dabarmu, su Walid suka karɓe ni, suka kuma tabattar mini da cewar na rasa Jauhar. Na burkice musu, amma suka riƙe ni suna kula da ni, kawai sai ga sanarwa daga hukumar 'yan sanda, wai a kamo ni, a raye ko a mace, da fari suka ce na gudu daga prsion, daga baya kuma wai an sake ni ba bisa ƙa'ida ba. Walid ya ce "Kome za ayi, ba zasu yadda a sake mayar da ni a kulle ba, sun san ba zan taɓa kashe 'yar madara ba. Na tarar da su da ɗan mama, na san shi tun da na taɓa yi masa rauni, shi ne ya bayar da gidan da muke zaune muke ɓoye. Idan nayi kamar na gaya musu, rayuwar da nayi ana bani training, sai na tuna aikin sirri ne, an gargaɗemu a kan haka, kuma bani da evidence ni kaina bani da tabbacin cewa a gaske nayi wannan rayuwar. Bana iya bacci, bana iya cin abinci, ga azababben ciwon kai, ga nauyin ƙirji, kawai na koma shaye-shaye fiye da da, duk da a wurin training ina shan sigari da wiwi, sai dai bana shan miyagun ƙwayoyi, ko giya. Amma bayan tabattar da mutuwar jauhar, na cigaba da shaye-shaye ina fatan ko haukacewa nayi, na manta da duk wata rayuwa, wadda nake tunanin gaske ce ko mafarki, amma kayan cajin basa ɗaukata. Ganin ɗan mama na din ga yi tamkar Nura, dan ba zai fi sa'ansa ba, ya din ga yi mini biyayya, hakan ya sanya nake son sa sosai, saboda su Walid kullum cikin faɗa muke, suna hana ni shaye-shaye. Shi kuwa samowa yake yi ya kawo mini, a hakan idan na bushi iska, sai na tafi gidana na dura ta katanga, na kan yi iya ƙoƙarina nayi kuka, amma bana iyawa, sai dai na yi ta jin ƙunar rai da bugun zuciya. Na kan yi yinƙurin zuwa na ɗauki fansar abin da madaki yayi mini, amma su Walid su hana ni, suka samo mini waya keypad suka bani incase ina buƙatar wani abu, basa nan, ɗan mama shi yake yi mini duk wata hidima, kawai wannan mutumin ya fara kirana, yana ƙara dagula mini lissafi. Kayan shaye-shayen ya zama basa ɗaukata, sai dai nayi ta tamɓele, suna iya ƙoƙarin su a kaina, amma ba sa yi mini abin da nake so. Damuwa shaye-shaye suka ƙara tsunduma ni a wani hali, har nake yinƙurin kashe kaina. Ashe duk wannan abun, mutanen nan suna bibiye da ni, da duk wani motsina, na din ga ƙoƙarin jami'an tsaron kawai su kamani, su yi duk yadda za su yi da ni, amma da nayi laifi, dan goge hanyar da za abi a kama ni. Walid ya zo ya bani labarinki, na ce ƙarya yake yi, cutata zai yi. Bai haƙur ba, ya kawo mini ke, kawai ƙwaƙwalwata ta bani cewar, an haɗa baki da ke an shirya wani abun ne, dan a kuma yi mini wani mugun abun, hakan ya saka na sanya miki ƙarfe ko zan ga ainihin wacece ke, dan na san jauhar ba ta kaiki girma ba, ba ta kaiki waye ba, kuma babu yadda za ayi ta ganni ta kasa gane ni. Amma da ki ka faɗi, ciwonki ya tashi, sai na ga kin koma ita sak, duk da ina jin haushin mata wasu lokutan, amma a sanadinta nake tausayin su, saboda tunawa da ita, na sai kayan treatment ɗin ta na asma, nake ajiyewa ina kallo, ina ganin kamar zata dawo. Shigowar ki rayuwata, ya ƙara rikita mini lissafi, Walid ya ce na sanar miki irin kamannin da ki ke yi da matata, na baki labarina, amma naƙi. Na cigaba da barazanar kashe ki, saboda na kasa tantance jauhar ce ke ko ba ita ba ce, nayi ta ƙoƙarin avoiding ɗinki, kar na aikata ɓarna, saboda babu in da ki ka bar ta, sai kuma daga baya na ga zuwanki wurina, yana rage mini damuwa, kamar ke kin fahimci halin da nake ciki. Rigar da ake ta bibiyata da ita, ta wancan aikin ce, dan an tura mini saƙon zasu tafi da ni, na ƙi kulawa, sai daga baya da na amince da ke, na ga dole ina buƙatar security ko dan lafiyar ki, na amince zan tafi nayi aikin, amma sai na samu nasara a kotu. Aka ce za a ɗaukar mini lauyoyi da zasu kare ni, zasu nemi a basu ni, su suyi na su binciken, su yi mini hukunci na ce ban yarda ba, ina da lauya, tsaro kawai nake buƙata a tsare mini lafiyarki. Suka yarda da hakan, amma da zimmar zan fara yi musu aiki. Daga nan barrack ɗin kano, suka zo suka tafi da ni, aka bani kayan aiki, ciki har da tab ɗin hannuna, da rigar aiki da ki ke ganina da ita, sai dai ba kowa ya san ma'narta ba, ciki har da su Walid. A yanzu haka ina karɓar salary, kuma ina aiki da NIA, ƙoƙarin ki ne zai sanya, na yi free na cigaba da aikina, akasin haka kuma, zan iya komawa prison ne, babu ranar fitowata, duk da ba zan ce ma ban yi shekarun nan a prison ba, tun da kauwwame ni aka yi, aka hanani dukkanin walwala. Nabila tayi ƙuri da ido tana kallonsa, cike da tsantsar mamakin duk wannan rashin mutunci, da cin mutuncin doka, a Nigeria ake aikata shi. Wani abun idan bai zo kanka ya faru ba, sai ka rantse da Allah ƙarya ne ba zai faru ba. Har gara shi, da aka fitar da shi daga prison ɗin, taimakon sa aka yi ta wani fannin, wasu kuwa canza musu gari ake yi gaba ɗaya, suje su yi rayuwarsu, saboda tsabar masifa, a prsion ɗin ma bin sa aka yi za a kashe. Gaba ɗaya rayuwar Viper gaba a baya take, sai dai ita ma tata rayuwar kusan haka. "Abla, talk please, jami'an tsaro na nemana, zan je a ɗauki statement, kuma dole sai da ke zamu tafi, dan Allah ki daidaita nutsuwar ki, yanzu rayuwata tana hannun Allah, tana hannunki, nayi rejecting support ɗin da za a bani a hukumance, na zaɓi cika miki alƙawarin da nayi miki, ba zan ja da baya na barki ba" Ta ɗago idanunta da suke tsiyayar da hawaye ta ce "Wacece ni? Kuma wacece jauhar?" "Ki na ji na? Shiyasa tuntuni nake jinjina yadda zan yi miki bayanin nan, ki nutsu ki karɓi ƙaddara a duk yadda zata zo miki" Nabila ta ware masa manyan idanunta, da suka yi jawur, ta ce "Ba ni ce jauhar ba, to ni wacece? Ko jauhar 'yar uwata ce? Dan girman Allah ka kaini gidansu na ga ko iyayenta ne, wataƙila muna da alaƙa" Ya girgiza mata kai ya ce "Babu tabbacin kina da alaƙa da ita, bata taɓa gaya mini cewar tana da wata 'yar uwa ba, ce mini tayi itakaɗai mahaifiyar ta ta haifa a gidan, ta fita. Amma ke babu abin da ki ka sani game da mahaifiyarki, da ahalinta?" Ta ja wata irin ajiyar zuciya ta ce "Idan ya kasance jauhar yar uwata ce, kenan ina da 'yar uwa ban taɓa ganinta ba, ban rayu da ita ba? An cutar da ni, wallahi an zalunce ni" Viper ya ce "Kar ki ce haka, ki bari sai mun tabattar tukuna, kuma wannan amsar dole 'yan gidanku ne za su bayar da ita, amma mu fara gamawa da wannan case ɗin, kiyi haƙuri" Tari ta fara yi, tana kuka ta ce "Ni gaba ɗaya baka yi mini adalci ba, ka ɓoye mini abubuwa da yawa, da yakamata na sani, sai yanzu zaka gaya mini. Ni ka rabu da ni ma ka ƙyale ni, ina ga nima haukacewar zan yi" Duk yadda Viper ya sauke jin kansa, yake rarrashinta, ta burkice masa, ta ce idan an ga dama a ɗaure shi da igiya, case ɗin nasa ma ta fasa, ƙarshe haka ya tashi ya rabu da ita. *** "Badi'a, anya ba zan gudu na bar ƙasar nan ba, ina daf da yin faɗuwar baƙar tasa, wannan yarinyar ta dage sai ta ga bayana ta kaini ƙasa, ya zan yi ne?" Badi'a ta ce "Naja, wallahi ki ka bari yarinyar nan ta ga bayanki, kin ɗuma asara" "Badi'a, kowace hanya ta toshe ta ko ina, duk masu goya mini bayan, sun ce wannan karon lamarin yafi ƙarfin su, shi kansa Indabo yana can Abuja, yana fuskantar tuhuma, EFCC sun dakatar da wasu daga cikin kadarorinsa, yana cikin tashin hankali, na rasa yadda zan yi". "Wallahi kina guduwa asirinki zai tonu, ki jira kiga iya gudun ruwansu, tun da haryanzu ba su ce komai ba, ba su tona miki asirin ba" Kamar ta fasa ihu ta ce "Yanzu jira zan yi sai sun fito sun tona ɗin? Ke kin san ba zasu bar ni ba, lallai ɗan hakin da ka raina, shi ke tsole maka ido, babu ƙoƙarin da ban yi na kawar da yarinyar nan ba, amma abu ya gagara, amma duk da haka ba zan zuba ido ba, sai na san abun yi". *** Abdul kuwa ya yi sintiri tsakanin Kano da Abuja, babu adadi, amma ya kasa ganin Indabo, hakan ya sanya ya tabattar wa da kansa cewar Indabon ne ya ɗauke ramma. Duk yadda mahaifiyar ramma, ta bugi cikinta, ramma ta nuna mata babu abin da ya faru, Abdul ajieta kawai yayi, duk da ya ce ya aureta. Maman ramma ta ce "Har na ji sanyi, dole a zo a raba auren nan, dama ba da yardata kawunki ya aurawa wannan tsohon mara mutunci ke ba, saboda kuɗi da tsinannen son abin duniya yayi mini haka. In sha Allah yaron nan sai Allah ya tozarta shi kamar yadda ya tozarta mu, sai Allah ya wulaƙanta shi, kamar yadda yayi mana" jin Addu'a ramma tayi har cikin zuciyarta, dan sai da cikinta ya motsa, tayi shiru bata amsa da Amin ba, ta san duk inda yake yana can hankali a tashe. "Amma ramma, kin tabattar ba abin da ya haɗaki da mutumin nan? Mutumin da yayi miki fyaɗe shi ne zai aure ki kawai ya ajiye ki?" Cikin tsoro da rashin gaskiy, ramma ta ce "Eh, ɓoye ni yayi saboda kar asirinsa ya tonu, cewa aka yi da ya kashe ni ma, shi ne bai kashe ni ba. Kuma wai ya biya mini kuɗin makaranta na cigaba har jami'a" "Allah ya kiyaye, ba ma buƙatar duk wani abu daga hannunsa, da haka zai yaudaremu, in sha Allah sai an hukunta shi, barrister nan tayi mini wannan alƙawarin, sai an gurfanar da shi, ya girbi abin da ya shuka, ga kisan kan da suka yi wa wannan tsohon, da suka ƙalawa sharri, Allah dai ya watsa shi, daga shi har wanda suke goya masa baya" Ramma ta kawar da zancen, ta hanyar cewa "Mama wai a nan zamu yi ta zama?" Ta ce "A'a, nima wannan Alhajin ne ya saka aka ɗaukko ni wai idan aka bar ni, nima za a iya cutar da ni, ban san zuwa yaushe zamu zauna a nan ɗin ba, amma ina ga da komai ya daidaita sai mu tafi" Ramma ta jinjina kai. Maman ramma ta bi ta da ido, ganin yadda duk jikinta yake a sanyaye, ta kalli fatar ramma yadda tayi haske take ta sheƙi. "Rahama" "Na'am mama" "Wai me ki ke ci ne a hannun nasa, na zata a wahale zan ganki, ki gaya mini tsakani da Allah idan akwai wani abu" "Mama babu komai fa, nifa tun da ya ajiye ni baya ƙasar, sai masu kula da ni" mama ta jinjina kai kawai, ba ta sake magana ba. Viper ya haƙura da azabar kishin da yake ɗawainiya da shi, aka yi zama na musamman da shi da Alhaji mu'zzam, da shugabannin sa, aka sake jaddadawa Al'amin, Alhaji mu'azzam tainakonsa yayi, kuma tare da haɗin kan Alhaji mu'azzam komai ya tafi daidai, kasancewar sa babban mutum a ɓangaren harkar tsaro. Sai kuma aka yi masa alƙawarin ba shi duk wata kariya, da shi da Nabila, tun da haka ya zaɓa, amma muddin suka yi failing a shari'a a kotu, babu wani abu da za a kuma sake yi masa. Ya ce ya amince, babu gudu babu ja da baya Nabila ce lauyar da zata tsaya masa. Sai dai Nabila gaba ɗaya ta hargitse, Viper ya kasa gane kanta, gashi an gayyace shi hukumar yan sanda, ya je ya bayar da bayani, amma Nabila fafur ta ce ba zata je ba. Sanarwa kuma ta fita, muddin Viper bai kai kansa ba, order kotu zata koma arrest order. Nabila na zaune, zuciyarta a cunkushe ta rasa abin da yake yi mata daɗi, lallai tana buƙatar ganin Abba, ko ta halin ƙaƙa Viper ba shi da niyyar yi mata bayanin abin da take son ji. Ta ga wayarta a gefen gadon da take kai, tayi sauri ta ɗauka, ta kunna tana dudduba saƙonni. A What's app ta tarar da message, wai gari ana ta yaɗa rumors, cewar Viper ya saceta, ba a san in da take ba, wasu suna Allah ya ƙara, wasu suna yi mata addu'a. Ta buɗe message ɗin Nasir, ta saurari voice message ɗin da ya turo mata. "Haryanzu wanda ki ke iƙrarin karewa, bai bayyana a gaban hukumar yan sanda ba, idan ya wuce wa'adin da muka bashi, order kotu zata sauya, ga shela da ake ta yi, na cewar ya sace ki, ba a san in da ki ke ba, ko a nan sunanki ya ɓaci, am did on you. Knocking aka yi, tayi shiru, dan ta zata Viper ne, ta ajiye wayar. Wani narkeken mutumi ne ya shigo, tare da barrister Habib, da sumayya, da kuma Walid. Zama tayi sosai tana kallonsu, sumayya ta ƙarasa ta zauna a kan gadon ta ce "Nabila, ya kike kina cikin ƙoshin lafiya?" Nabila ta jinjina mata kai. Mutumin ya ce "I salute you barrister, kallabi tsakanin rawuna" yayi maganar cikin gurɓatacciyar hauss, amma da alama ya ji hausa. Ta ɗan yi murmushi yaƙe, ta kalli Walid ta ce "Oga walid" "Na'am barrister, ya ki ke ya ƙoƙari?" "Alhamdilillah" ta din ga bin su da ido, dan bata san dalilin zuwan su duka ba. Walid ya ce "Barrister, na san mun yi miki laifi, tun da fari na so Viper yayi miki bayani, amma yaƙi, kin san shi wasu lokutan da taurin kai, kuma na san kin yi haƙuri da shi, amma dan Allah ki janye batun cewar ba zaki tsaya masa ba, ki yi haƙuri dan Allah, ba zamu iya jure ganinsa ya koma prison ba, kiyi wani abu a kai, wanda kuke ƙalubalanta, suma ba zasu zauna haka ba, dole zasu yi ƙoƙarin yin wani abu suma, ki taimaka" Ɗaya mutumin ya ce "Duk wani support da zamu ba shi a hukumance, yaƙi yarda, ke kaɗai ce hope ɗin sa, kar ki ce a'a, kiyi haƙuri, a ƙarasa wannan case ɗin, sai koma menene ya biyo baya" "Meyasa ya ɓoye mini abubuwa irin wannan?" "Tsarin aikinmu ne a haka, haryanzu ke kaɗaice lauyar sa, ke ki ka sani, su kansu yanzu da muka zo tare ba komai suka sani ba, ga abokin aikinki, dole kina buƙatar sa, ga ƙawarki kina buƙatar ta, ga abokansa da sun san komai" Barrister Habib ya ce "Ga case ɗin ramma ma" Mutumin ya ce "Yess, ke fa yanzu idon duniya yana kanki, ba laifinsa bane, kin san ba mai yawan magana bane ba, kuma tsarin aikinmu ne, yanzu abin nan da ya gaya miki, zai iya zama da hukuncin kisa a kansa, banda mun san a situation ɗin da yake" Walid ya ce "Yana asibiti ma, ciwon cikin nan da yayi kwanaki ya kuma tayar masa, hantarsa ta kumbura, yana asibitin sojojin nan da aka ɗaukko ki" Nabila ta numfasa, ta ce "Muje zan ganshi, kuma ina son zuwa office ɗina, zan koma aiki" Mutumin nan ya ce "Is ok, zaki koma bakin aikinki, amma a ƙarƙashin kulawar mu, ƙasarmu na san rayuwar Viper" "Amma ku ka bari ya kusa haukacewa, aka ɓata masa suna" mutumin yayi murmushi ya ce "We are trying our best now" Sumayya ta ce "Nabila ina son magana da ke fa" "Ni da nake kare ɗan ta'adda, me ki ke so a wurina?" Sumayya ta yi murmushi ta ce "Arfan Abbanta, an buga dake an barki, batutuwa ne masu muhimmanci, amma sai kin saukko tukuna" A cikin wata rantsatsiyar mota, aka ɗauki Nabila da sumayya, da barrister Habib, suka tafi. Liti ya ƙarewa ɗan mama kallo ya ce "Ɗan mama, ni haryanzu mamaki nake yi, yaushe Viper ya san wannan mutanen bamu da labari ne? Wai naga sojoji ne suke kula da shi, duk ka munafunce mu" "Nima ban san meyasa ba" "Ƙarya kake yi munafiki, ka san komai, meye haɗin Viper da sojoji? Ko ka gaya mini ko na ɓulaka da wuƙa" Ɗan mama ya ce "Wallahi oga liti muka yi misbehaving, zanemu za ayi daga ni har kai a barikin nan, dan Allah kayi haƙuri ka rufa mana asiri" "Ni haryanzu tsoro nake ji, idan ba haɗa kai aka yi da kai, ake son a kashe mu ba, ko a haɗamu a cikin yan boko haram ace duk su ne ba, gaba ɗaya baka da imani ɗan mama, tsawon lokaci kana jakadancin munafunci" Suna cikin maganar, su Nabila suka shigo wurin, ba wanda ake bari ya shiga wurin Viper, su liti ma a waje suke. Aka ce Nabila ce kawai zata shiga wurin Viper. Ta taka a hankali ta shiga, ta tarar yana kwance, likita yana yi masa allura ta cikin cannula. Suka gaisa da likitan, ya gama yi masa ya fice, ta zauna ta kalleshi ta ce "Effect na shaye-shaye yana ta bibiyarka" ya yi shiru yana kallonta. "Idan ɓoye mini waye kai, ba laifinka bane tsarin aikinka ne, ni kuma ɓoye mini wacece ni, laifinka ne da wasa da hankalina. Ba zan watsar da alƙawarin da nayi maka ba, gobe in Allah ya kaimu zamu je station, zamu bayar da statement, amma bisa ga sharaɗi ɗaya da sai ka yadda da shi" Ya lumshe idanunsa ya buɗe yana kallonta. "Am talking to you". "Viper zaki sawa sharaɗi?" "Your freedom depends on me, so watch your tounge" "Send me back to prsion if you like, i am still Viper, the most dangerous snake" "A heartless spy" Ya yinƙura ya tashi zaune yayi murmushi ya ce "I admit it, am heartless" "Dole ka amince da sharaɗina Viper, akasin haka kuma........ Ayshercool 08081012143 81 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* Shiru tayi ganin irin kallon da ya yi mata, a take jikinta ya hau rawa, ta haɗiye maganar da take son yi. Ya jingina yana kallonta ya ce "Ina jinki, sharaɗin menene?" Ta girgiza kai ta ce "Shikenan kawai, yakamata mu fara zuwa mu sake ganin madaki, an ce yana asibiti, a hannun jami'an tsaro, yakamata mu je mu ganshi, kafin mu haɗu gaba ɗaya a gaban yan sanda" "Menene sharaɗin naki?" Ta ɗan kalle shi ta ce "Bakomai, ya wuce kawai" ta yinƙura zata tashi, ya mayar da ita ya zaunar da ita, yana bin fuskarta da kallo. "Kawai kin zaɓi ki wahalar da ni, saboda kin ga ina lallaɓaki ko?" Ta girgiza kai Viper ya ce "Haka ne mana, i can give up the trial, na koma prison kawai, i can do it" Jiki a sanyaye ta ce "Am just curious to know who i am, ina son sanin mahaifina, da 'yan uwana idan ina da su, amma bana fatan ace ina da alaƙa jauhar matarka" Da sauri ya ce "Why?" "An gaya mini mahaifina yana da mata da yara, ya auri mahaifiyarmu, muddin jauhar yar uwata ce, zai iya yiwuwa cikinmu ɗaya, ta mutu ba tare da na taɓa ganinta ba" tai maganar tana zubar da hawaye. "Kin ga babban dalilin da ya sanya, na cigaba da ɓoye miki abubuwa da dama, you will lose confidence. Babu tabbacin kina da alaƙa da jauhar, kuma dolena cika alƙawarin da nayi miki, ki kwantar da hankalinki" kamar ya tunzurata, ta cigaba da kukan. Yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Bana barin 'yar madara ta zubar da hawaye, muddin kina kuka a gabana, matata nake gani, zan iya rungumarki at any time na ce zan rarrashe ki, ki rufa mini asiri kar ki saka na aikata ɓarna, kin ga daga nan kuma ba lallai na tsaya a nan" da sauri ta ja da baya tana kallonsa, tsaf zaka rantse ka ce baya magana. Ta ce "Ammm yaushe zamu je mu ganshi?" Viper yayi murmushi ya ce "Za ayi mini allurai anjima, sai mu je kawai" Nabila ta ce "Ka ji sauƙi ne?" "Idan aka yi mini allurai ina jin daɗin jikina, daba da shaye-shaye sun yi mini mugun tabo, illoli ko ta ina" "Kayi ta istigfari, Allah ya yafe maka ya sassauta maka, bari na je waje" ya jinjina mata kai alamar to. Ta fito ta tarar da su, ta kalli barrister Habib ta ce "Yaya, zamu je mu ga ɗaya daga shaidun da muke da su ne, gobe in Allah ya kaimu zamu je wurin jami'an tsaro" Habib ya ce "To shikenan, jikinsa sa sauƙi amma?" Ta jinjina kai alamar eh. Sumayya ta ce "Ni dai sonake naga Vipern nan, amma Allah bai yi ba, zan koma ana nemana, amma Nabila na gaya miki mahaifin sa yana ta sintiri, yana so na haɗaki da shi, neman ɗansa yake ido rufe" Jiki a sanyaye Nabila ta ce "Ki rarrashe shi, yayi mana afuwa zuwa mu kammala shari'ar nan, Viper ba zai yadda su haɗu yanzu ba". "Amma Arfa meke damunki ne? Ko wani abin suke yi miki da ba kya so?" Nabila ta girgiza kai hawayen da ta ke ƙoƙarin tarewa, suka zubo mata. Hankali a tashe Sumayya ta ce "Nabila menene?" Nabila ta ja hannunta suka koma gefe, ta ce "Sumayya, matar Viper da aka kashe, ina kyautata zaton ina da alaƙa da ita" Sumayya ta ce "Ta ina?" "Yanzu na san ko na ce ya bani hotonta, ba zai bani ba, idan ki ga ganta rantsewa zaki yi, ki ce ni ce a jikin hoton" "Ke Nabila bana son shirirta dan Allah, saboda soyayya ta rufe miki ido, har kin fara kalen dangi" A hasale Nabila ta ce "Sumayya yaushe zaki din ga ɗaukar maganganuna serious ne? Kodayeke shikenan, daga baya idan komai ya bayyana, zaki gane idan ma ƙarya nake, idan ma gaskiya nake faɗa, ki je kiran da ake yi miki" Sumayya ta bi Nabila da kallo har ta bar wurin. Suna tafe a hanya, Nabila take tunanin lokacin da take takurawa Nasir, tana tambayarsa me zata yi, wanda zai saka tayi suna sosai ta zama kamar bunkure, ya ce mata ta nemo masa Viper. Ta din ga bin yadda abubuwa suka din ga faruwa daki daki, ita kanta ta san ƙudura da ikon Allah ne kawai da ya ƙaddara sai ta haɗu da Viper. Da ta din ga lissafa rashin hankali da wautar da ta din ga yi, tana yawon nemansa, yana iƙirarin kasheta, amma tana nace tana bibiyarsa kamar mayya har zuwa wannan lokaci, abun lamari ne na Allah kawai. "Amma daga can, yakamata muje ku gaisa da mahaifiyar ramma" Ya ɗago ya kalli Nabila ya ce "Bana son haɗuwa da mutanen da na sani, suna yi mini kallon ɗan ta'adda" Nabila ta girgiza kai ta ce "Ba kowa ne yake yi maka kallon hakan ba, abin da yakamata ne, mussaman da iftila'in nan ya faɗawa ramma" yayi shiru bai ce komai ba. Har ɗakin da madaki yake aka kai su. Tare da Viper suka shiga, suka tarar da shi a kwance, duk jikinsa sara da suka, da rauni, ɗakin sai wari yake yi. Babban abin da ya bawa Nabila mamaki bai wuce duk jikin madaki raunukan nan sun yi kore ba, maimakon ja, irin na ciwo. Hatta fuskarsa sara ne, kamanninsa sun sauya daga shi sai ɗan wando. Nabila ta dubi jami'an tsaron da suke tsare da shi ta ce "Yanzu a haka yake? Ana duba shi kuwa?" "Eh, likitoci na duba shi, yana da ciwon suga ne, dan haka wannan raunukan ba zasu warke ba, sai dai ayi ta treatment a haka". "To wannan tayaya zamu je da shi kotu, yana magana ma tukuna?" Madaki ya buɗe ido da kyar, yana kallonsu. Viper yayi murmushi, dan ya san ba ciwon suga bane kawai, russia da yayi amfani da ita, wurin karya sihirin da yake amfani da shi ne ya janyo haka, duk wani rauni da ya ji, muddin da ƙarfe ne, ba zai warke ba. Wancan karon ma Viper shi yayi sponsoring yanke ƙafar madaki. Viper ya ce "Ya kake kallonta, haryanzu kana tunanin wadda ka kashe ce ko? Nayi mamaki da na turo maka ita da farko, ka iya jurewa baka yi wani abu ba. Kodayeke namiji idan ya kai namiji, baya tsoro baya nuna gazawa. Ina yi maka albishir da sai ka ruɓe a raye, kafin ka mutu, dan idan ka mutu yanzu hutu ne. Naka ƙarshen ya fi na kowa muni. Baka aikata alkhairi ba, baka bar wani baya mai kyau ba, babu ɗa babu jika, sai tarin zunubi da haƙoƙƙin mutane. Ga lokaci ya ƙure da zaka bi su yawon neman yafiya. Ka zo a banza zaka koma a wofi, ina fatan sunana da yake gadon bayanka ba zai ruɓe ba, zaka koma ga Allah da shi, duk da kome zan yi maka, ba zan huce zaluncin da ka yi mini kashi-kashi ba. Da farko yayana, na biyu ubangidana, mafi muni kuma matata da ɗa na, wata shari'ar sai a lahira, duk abin da zan yi maka, ba zan bi wa yar madara hakkinta ba, Allahn da yayi ta shi zai saka mata" yayi maganar muryarsa na rawa. Madaki ya ƙure su da ido. Nabila ta girgizawa Viper kai, cikin matsanancin tausayin sa, juyawa yayu yana haɗiye hawayen da yake shirin zubo masa. "Vi, shaidar da muke da shi, ɗaya yana kwance ba zai ma taɓa yi mana amfani ba, ba magana zai yi ba, dole muna buƙatar wata ƙwaƙwƙwarar shaidar" "Kamar wa kenan? Wa zamu samo?" "Muna buƙatar, ko daga cikin maƙwabtanku, ko makamancin haka" Viper ya ce "No, ki rabu da wannan mutanen, mu bari gobe in Allah ya kaimu sai mu ga yadda za ayi". "Muna buƙatar iyayen jauhar a case ɗin nan" "Meyasa?" "Saboda shaidunmu su zama masu ƙarfi, bana son a ja shari'ar da yawa" yayi mata shiru bai sake cewa komai ba. Nabila har system ɗin ta aka kawo mata daga wurin aiki, barrister Habib ya kawo mata. Tayi mamakin yadda tun da ta kunna wayarta, daga gidansu babu wanda ya neme ta. Dan haka ta kira Abba, sai da ta kusa katsewa, sannan ya ɗaga. Ta ce "Abba ina wuni?" "Lafiya ƙalau Nabila, yau kin tuna da ni kenan?" "A'a Abba, wayar ba ta hannuna ne, yau aka bani ita" "Kin ga abin da taurin kanki ya janyo mana ko? Ƙiri-ƙiri an ɗauke ki, an kai ki in da ban sani ba, da sunan an kauwwame ki, ban isa na ganki ba" Cikin mamaki Nabila ta ce "To ai Abba Sumayya ta zo in da nake, barrister Habib ma haka, kuma dama na ce zan koma bakin aiki, ina son zan dawo gida" "Ai kin ga da baki bijirewa umarnina na cigaba da kare mutumin banza ba, da ba ayi haka ba. Ki je Allah ya taimaka" ya kaste wayarsa. Nabila ta bi wayar da kallo, ta rasa abin yi gaba ɗaya. Nasir kuwa ya kasa ya tsare, muddin Viper bai bayyana a gaban yan sanda ba, sai ya kama shi, ya ɗaura aniyar ko ta wani hali sai ya kai Nabila ƙasa da Viper, Viper yake son nuna wa iyakarsa, ko dan saboda wulaƙanci da gadarar da yayi masa. **** Sumayya ce da safe ta buɗe gidan radiyo da safe, tana amsa gaishe-gaishe, masu sauraro suke tambayarta ina Nabila da gaske an yi garkuwa da ita. Sumayya ta ce "Haƙiƙanin gaskiya, ba wanda yayi garkuwa da Nabila, yanayin jiki da jini, ayyuka sun yi mata yawa, kuma ba ta ɗan jin daɗi, dan haka da komai ya lafa za a ji ta dawo" Message ɗin Nabila ta gani, a kan su haɗu a police station, tana son su zama witness, zasu je da Viper a ɗauki statement ɗin sa. Sumayya ta riga su Nabila zuwa, da ita da murtala. A wata irin zuƙeƙiyar mota aka kawo Nabila, da Viper da su Walid. Nabila ce ta fara fitowa, su Walid ma suka fito. Sumayya ta ce "Ki ka ce na zo da wuri, amma sai yanzu ku ka ƙaraso" "Malama ba wani daɗewa fa muka yi ba, yaya murtala ina kwana" Ya ce "Lafiya ƙalau, ya ki ke ya hidima" Alhamdilillah. Sumayya ta ce "Ina Vipern ne? Wanne shi a nan?" Tayi maganar tana nuna su Liti. Nabila ta yi murmushi ta ce "Wane mutum, yana cikin motar, sai ya gama mulkin zai fito" "Kai ni nayi neman suna, naje na gaishe shi" Nabila ta yi dariya ta ce "Idan yayi miki halin, zaki gane baki da wayo, ki bari zai fito da kansa. Motar barrister Habib ma ta iso harabar wurin state CID ɗin, yayi parking ya fito, suka gaggaisa, amma madugun yana ƙame a cikin mota, yana kallon su ta cikin glass. Can kuma da ya gama abin da Allah ya nufe shi da yi,  ya fito daga motar. Ƙaton tabon da yake gefen wuyansa ya tabattar wa Sumayya shi ne Viper, duk rawar ƙafar da take yi zata ga Viper yau, sai bakinta ya mutu, ta zubawa sarautar Allah ido. Ɗan ƙarewa harabar wurin kallo yake yi, yana tuna adadin zuwansa wurin nan, tun jauhar na raye yake zuwa, da aka kasheta ma, nan aka kawo shi, aka din ga gana masa azaba. Tinkis-tinkis, ya fara tafiya yana bayar da faɗi. Barrister Habib ya miƙa masa hannu, suka gaisa ya ce "Ya jikin, an ce mana baka ji daɗi ba jiya" Viper ya ce "Eh, ina ta fama da hanta, sai fatan Allah ya sa mu yi kyakywan ƙarshe" Ɗan mama ya ce "A'a Master ba yanzu ba in sha Allah" Viper ya galla masa harara. Liti ya ce "Wannan zaƙal zaƙal ɗin da ka ke yi, ba zai hana aci ubanka, a hukuntaka ba, gara ai maka hukunci a duniya, tun kan ka je lahira da laifin munafunci" Nabila ta ce "Viper, ga yar uwata, sumayya T ladan" Ya jinjina kai ya ce "Yarinyar indabo" yayi maganar yana mayar da hankalinsa kan Walid da yake yi masa magana. Zata yi magana, Nabila ta hana sumayya magana. Nasir ne ya shigo, wurin shima, da tasa tawagar, yana tafe ana sara masa, yana wani basarwa. Sai da ya ɗan tsaya suka yi kallon kallo da Viper. Sumayya ta kalli damtsensa na hagu, nan ma wani tabon ne, da alama an taɓa yi masa ɗinki a wurin, gefen kansa ma, ya wani shata kai ka zata aski ne aka yi masa a haka, amma sara ne. Kai da ganinsa ka san an sha gwagwarmaya. Nabila ta ce "Vi, dan Allah na san kai ba mai magana bane, sai abin da na amince kayi magana zaka yi, banda hasala da saurin fushi dan girman Allah, kar ka yi wani abu da zaka janyo mana matsala Please". Shafa ƙeyarsa yayi yana kallonta. "Bamu da ƙarfi, bamu da tsumi bamu da dabara, sai a wurin Allah, muyi ta addu'a" Ya jinjina mata kai, suna tafe, ya ga ta koma jauhar, lokacin da tayi belinsa da kyar, ta riƙo hannunsa suka bar wurin suna kuka. Ɗan sandan ya kalle su ya ce "Waɗan nan fa?" Nabila ta ce "Ni da wannan lauyoyin sa ne, wannan 'yan jarida ne, wannan kuma suna cikin shaidunmu" Mutumin ya jinjina kai, can aka fito da lakwari, ya rame ya fita hayyacinsa tamkar lagwani, aka riƙo ƙugunsa, aka fito da shi. Viper ya ƙure shi da ido, yana jin tamkar ya ƙwaci bindiga ya harbe shi. Ɗan sandan ya kalli Viper ya ce "Ina tayaka murna, kotu ta hana kamaka, duk da ba a nan take ba, an danne bodari ta ka" yanayin zaman da Viper yayi, kai baka ce da shi ake magana ba. "Meye cikakken sunanka?" Nabila ta ce "Sunansa Al'amin Ibrahim" Nasir da yake wurin ya ce "Bashi da baki ne?" "Doka ta bashi damar yin shiru, lauyoyin sa su yi magana" ya kalli Nabila ta kalle shi. Aka juya aka karɓi sunan lakwari ma. "Menene ƙorafinka?" Viper ya kalli Nabila, ta jinjina masa kai ya ja wasu second ya numfasa ya ce "Sun shiga gidana, da misalin ƙarfe uku saura na daren alhamis, shekaru shida da suka gabata, suka shaƙa mini abu, suka kashe matata, ta hanyar kayar da ita a kan cikinta, bayan sun bugar da ni". Nasir ya ce "Amma shaidu sun tabattar da cewa kana ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, su ka sha ka kasheta" Viper yayi shiru yana kallonsa, Nabila ta ce "Wane shaidun kenan? Nan ba zaman kotu muke yi ba, statement muke bayarwa" Nasir ya kalli Nabila, tamkar an canzata zuwa wata daban ba Nabilansa ba, yadda take yi masa martani da zuciya. "Meye haɗinka da su, da har suka shiga gidanka suka kashe maka mata?" Viper ya nuna lakwari, ya ce "Shi zaka tambaya, ban san laifin da nayi musu ba" Aka tambayi lakwari, amma lakwari ya kada baki ya ce "Viper ƙarya yake yi masa, ba su shiga gidansa ba, basu kashe masa mata ba" Taka ya fara harzuƙa, amma Nabila ta dakatar da shi. Walid ya ce "Yallaɓai, mune abokan harƙallar Viper, tare muke sha da fataucin wiwi, Viper ya kan sha ƙwayoyi amma ba ko yaushe ba, kuma mu abokansa da maƙwabtansa shaida ne, na matarsa ta saita shi a hanya, kafin su kasheta, dan kuwa a lokacin sai da Viper ya hana sayar da wasu kalar ƙwayoyi, a unguwar da yake da kewayenta". Nasir ya kalli Walid ya ce "Ikon Allah, daina shaye-shaye fa ba abu ne mai sauƙin da ka ke tunanin, abu ne da zai daina farat ɗaya ba. Abu ne da yake buƙatar dogon lokaci, wani ma har da likitocin ƙwaƙwalwa kafin mutum ya daina, ta yaya zamu yarda da cewar Aminu ya daina shaye-shaye kuma bai yi shaye-shaye ba a wannan ranar?" Liti ya ce "Sun je Asibiti da matarsa, ni na raka su, aka ce za a yi mata inducing, bamu koma gida ba sai bayan ƙarfe goma na dare, suka ajiyeni suka wuce gida a adaidaita sahun wani ɗan unguwarmu. Viper bashi da wani wurin zuwa sai wurinmu, bashi da wasu abokai sama da mu, tare muke shaye-shaye, irin abu ɗaya muke sha, dan haka Viper baya cikin nutsuwar sa, bai yi shaye-shaye ba ranar, suna fargabar inducing da za ayi wa matarsa". "Malam shi mai shaye-shaye, kullum yana buƙatar samun sauyi, da samun abin da zai bugar da shi, fiye da wanda yake amfani da shi, dan haka zai iya yiwuwa ya samu wani abun bai sanar muku ba" "DSP Nasir, ya sunan abin da Viper ya sha ne ya bugu ya kashe matarsa?" "Hodar iblis ce, aka haɗata da wasu sinadarai, kuma a binciken da muka yi, an taɓa kama shi da cocaine a gidansa" "Tayaya karabutin ɗan daba zai iya ta'amalli da cocaine a ganshi a haka? Ina gwaje-gwajen likita da yayi, ya tabattar da cewar ya ga cocaine a jinin Viper? Ko kuwa kawai da ka ake cewa ya sha cocaine?" "Wanda kuke tuhuma, bai amsa cewar shi ya aikata ba, kin san hakan dai-dai yake da baku da hujja" Ɗan mama ya ce "Mu na da ita" gaba ɗaya suka kalle shi. "Ina daga cikin yaran madaki tsageru, Viper ya taɓa illata ni, daga baya yayi mini nasiha, ya biya kuɗin da aka yi jinyata. Kwangilar kisan Viper aka bawa su madaki, aka haɗa musu da abin da suka kashe shi, saboda sun ce ba zai mutu ta daɗi ba, saboda yana da ƙarfi sosai. Da madaki, da lakwari, da wani ana ce masa ɗan fari, da gulafa, su huɗu su ne suka je gidan Viper. Kuma saka su aka yi, wani ne ya saka su". "Waye wanin?" "Ban sani ba, su za a tambaya, amma ina da hujja, duk da ɗan fari an kashe shi, amma gulafa lagos ya gudu bayan an biya shi kuɗin aikinsa" Yan sandan suka ce "Ɗan mama ma ya shiga cikin suspect, tun da a gabansa aka shirya komai, bai sanar da hukuma ba" A take Viper ya rikice ya ce "Ba zai yiwu ba, babu ruwan ɗan mama a cikin wannan maganar" Ɗan mama ya ce "Oga Viper, kar ka damu, zan zama cikin shaidu" Liti ma rikicewa yayi, ya ce "Ɗan mama wane irin shirme ne wannan kayi haka?" Nabila ta ce "DSP, ba fa zaman kotu muka zo ba, bayar da statement muka zo yi" "Ɗan sanda baya wasa da duk wani abu da zai iya zama hanya ce ta kama mai laifi, hanyar da kuka ɗauka ma, idan baki yi wasa ba, zata sadar da ku zuwa ga baƙar duhuwa" Ɗan mama ya ce zai yi magana da Nabila, yayi mata raɗa a kunnnenta, hakan ya sanya ta yi ajiyar zuciya ta ce "Na fahimta sosai, in sha Allah muke da nasara". Sumayya kanta tayi mamakin yadda Nasir gaba ɗaya ya canza, muraran ya fito da adawar da yake yi da Nabila. Ta sake keɓewa da barrister Habib, suka yi rubuce-rubuce, suka gama bayar da statement, suka tashi suka fita harabar wurin. Hankalin Viper ya ƙi kwanciya, ganin an kama ɗan mama, sai da Nabila tayi masa bayani, sannan ya ɗan samu nutsuwa. Nabila na fitowa, Nasir ya sha gabanta ya ce "Ki zo ki wuce mu tafi gida" Nabila ta kalle shi ta ce "Wane gidan kuma?" "Gida nawa ne da mu? Ko kin zaɓi Abba ya cigaba da fushi da ke? Ki je wurin da ba wanda ya san in da ki ke? Abba ya iya yarda ki tafi wurin da bai sani ba, ya ƙyale ki da halinki, hakan duk bai dame ki ba?" Nabila ta girgiza kai ta ce "Ko kaɗan, Abba baya fushi da ni, zigar da kake yi masa ne da kai da mahaifiyarka, ya sanya ya ɗauki zafi, amma na san yafi kowa fahimta ta, kuma zai fahimce ni. Kuma a barikin sojoji nake zaune, duk lokacin da ka buƙaci ganina zaka ganni, daga nan wurin aiki za a kai ni, barrister Habib sumayya, duk suna zuwa wurin da nake. Dan haka ka daina aibata ni, da cigaba da danganta ni da mummunar ɗabi'a, dan na san abin da ka ke yinƙurin yi kenan". Viper ya ƙaraso in da suke tsaye, ya ce "Ga abokin aikinki nan, zaki iya bin sa ki je office, in sha Allah you are safe" Ta jinjina masa kai ta ce "Zamu je mu ga ramma ma, daga nan na ji ina aka tsaya da batun kama mutumin nan, amma yakamata ka je ku gaisa da ita, kaga yarinyar ma, tun da kai yaya ne a wurinta, a yan uwanta babu wani wanda yake zuwa wurinta" Viper ya ɗan gyaɗa kai ya sakar mata wani irin murmushi ya ce "Zan je in sha Allah, tun da ke ce lauyata, kuma lauyar su, abin da ki ka ce ai shi nake yi ko?" Sai da Nabila ta tsaya tana kallonsa, cikin mamaki. Ya sake cewa "zaki iya tafiya, take care, my only hope" yayi maganar yana cigaba da yi mata murmushi, Nasir kuma ya sandare a wurin kamar katako. Nabila ta ce "To daga nan ina zaka je? Kar ka yi wani wurin" "Za a zo a ɗauke ni, ki tafi kawai tare da su Walid zamu tafi". Cikin damuwa ta ce "Kar na tafi fa su kama ka". "Babu hannun da zai iya kama wannan ƙarfen ba, ku tafi kawai" Nabila ta tafi tana waiwayensa. Tsananin mamaki ya kama Nasir, kenan Nabila son mutumin nan take yi, abin da ya gani a idonta, tsantsar soyayya ce. Ya tsura mata ido, har ta shiga mota, ita da sunayya su ka bar wurin, murtala ya hau babur ɗin sa ya tafi, Viper mayar da idanunsa kan Nasir ya ce "Malam, akwai mutanen da suke ajiyar Allah ne, duk tsanar nan da ka yi mini, na riga na fi ƙarfinka, babu yadda zaka yi da ni, takura mata da hura mata wuta a kaina, da ƙuntata mata a kaina, ba zai haifar maka da komai ba, sai zunzurutun ƙiyayyarka a wurinta. Ka san meyasa dalili biyu ne, a yanzu a wannan duniyar da nake ciki tafi kowa sanin waye ni, kuma babu wani abu da take tausayi kamar ni, kuma ka san menene ma'anar tausayi a wurin mace. Abu na biyu kuma wannan, mussaman saboda na haɗu da kai na baka, na cigaba da yawo da shi". Ya zaro envelope daga aljihunsa, ya ce "Na bata saƙo, ta kai muku gida, kun yi burus da ita, kun yi mata furucin ta je ta nemi mahaifinta, na gaya maka na fiku buƙatar ta, kuma lokaci yayi da zan biyata ladan aikin da tayi mini, ko kun shirya hakan ko baku shirya ba, dan haka shawara ta rage ga mai shiga rijiya". Ya danƙawa Nasir envelope ɗin ya ce "Gashi nan, mu haɗu a zama na gaba, ko kotu, ko a mafitar makomar Nabila" ya juya ya nufi in da su Walid suke. Nasir ya rasa meyasa baya iya kataɓus idan yana gaban Viper, yayi ta ci masa mutunci yana tsaye yana kallon sa. Liti kamar yayi kuka, ya ce "Ɗan mama, ɗan kut...... Saboda hauka da yarinta, ya ja an kama shi, uban waye ya gaya masa zaman wurin nan lafiya ne? Allah kaɗai ya san izayar da zasu yi masa, yanzu za a haɗa shi da masu kisan kai, na jakai zasu din ga naɗa masa wallahi wawa kawai" Viper ya ce "Mu tafi" "Mu tafi ina mu bar wannan banzan?" Walid ya ce "ashe dai kana son sa?" "Ba wai son sa nake yi ba, tausaya masa kawai nake yi, gaba ɗaya gaɓo ne" Viper ya dafa kafaɗar liti ya ce "Duk cikin plan ne, ka kwantar da hankalinka, ba abin da zai same shi in sha Allah" *** Sumayya suna tafe a hanya, suna hira da Nabila, ta ce "Subhanallah, Nabila kin ga wata ƙira ta manya, ga mulki wai kuma ɗan daba, gaskiya ya ci sunansa Viper, bala'i" "Ya maganar mahaifinsa da ki ka yi mini?" "Na gaya masa saƙonki ai" Nabila ta ce "Idan mun gama da wurin su ramma, zan ganshi" Sumayya ta ce "Da gaske, zaki haɗa shi da Vipern?". Nabila ta ce "Eh, zan haɗa su, zan yi uniting uba da ɗa, ko me hakan zai janyo kuwa" "Kina nufin akwai matsala kenan?" Nabila ta ce "A'a karki damu" Da hanzari Ramma ta ƙarasa suka rungume juna da Nabila, Nabila ta ce "Rahama, barka da arziki ban samu na zo na duba ki ba" "Bakomai Anty, na gode sosai da sosai Allah ya saka miki da alkhairi" Nabila suka gaisa da maman ramma, ta ce "Rahama ga masoyiyyar ku, Sumayya T ladan" Ramma ta ce "Anty sumayya ya aiki?" Sumayya ta ce "Alhamdilillah, ya fargaba kuma, Allah ya kiyaye gaba" Maman ramma suka gaisa da barrister Habib ma, tana tayi masa godiya, ta ɗaukko wa Nabila takarda, an yi stapling ɗin ta, ta ce "Gashi aka kawo, tasatasan da aka yi wa ramma ne, da aka ɗebi jininta, bayan an kawota, aka ce kar a buɗe ke za a bawa, tun da ke ce lauyanta" Nabila ta karɓa ta na faɗin "Ai yana daf da zuwa hannu, mun gama sbirya komai ta buɗe takardar tana dubawa, komai na ramma lafiya ƙalau, sai dai ga tes ɗin ciki ya fito rangaɗau". "Ina fatan babu matsala dai ko? Babu ƙanjamau ko wani abu?" Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Eh komai lafiya, amma rahama ɗan zo mana" Ramma ta tashi suka koma gefe, ta kalli ramma ta ce "Rahama kin san kina da juna biyu?" Ramma ta jinjina kai alamar eh. "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" "Dan Allah anty kar ki gaya wa mama" "Rahama dole a mata, dole ta sani fa" Cikin kuka ramma ta ce "Dan Allah ki rufa mini asiri" Ta kamo hannun ramma suka dawo falon, ta kalli mahaifiyar ramma ta ce "Maman ramma, da gaske kin tabattar ya aureta?" Jiki a sanyaye ta ce "Haka wan babanta ya gaya mini, meyafaru?" "Akwai matsala, sakamakon nan ya nuna akwai ciki fa" Sosai Nasir yake gudu, cikin matsanancin tashin hankali, ganin hoton da Viper ya bashi, hotonsa shi da jauhar. Ko rufe motar bai yi ba, ya fita ya faɗa cikin gida. Sai da Abba baya nan, ya din ga kallon hoton, cikin fargaba, kenan wannan ce ake dambarwa a kan kisanta? Saboda yanayin yadda suka yi hoton, ya tabattar da mata da miji ne. Lallai akwai gagarumar matsala. "Wai wannan wane irin mutum ne? Kenan ya san komai, shiyasa yake ziga Nabila? Akwai Matsala...... Ayshercool 08081012143 82 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* Nasir ya cigaba da jujjuya hoton, ya fita ya tafi sashen mama, ya tarar da ita tana cin abinci, amma ya rasa me zai ce mata. "Lafiyarka kuwa?" "Eh lafiya ƙalau, shigowa nayi kawai mu gaisa" "Kuma sai na ganka a haka kamar mara gaskiya, gaisawar da muka yi da safe fa?. Amm ya ake ciki ne? Ka haɗu da ita ɗin?" Ya jinjina kai ya ce "Eh mama, mun haɗu ƙarewar rashin kunya, tare suka je da gayen" "Hmm ai na sha gaya wa mahaifinku, gurbin ido ba ido bane ba, ai yanzu gashi nan ya fara gani. Ni dai ka yi iya yinka kar yarinyar nan tayi galaba a kan ka" Ya jinjina mata kai kawai ya fita. Wiwi ramma take kuka, mamanta ta ce "Ramma, kin munafunce ni, na ce miki babu abin da yaron nan yayi miki, ki ka ce mini eh, amma kawai sai na tsince ki da ciki? Baki kyauta mini ba" Ramma cikin kuka ta ce "Dan Allah mama ki yi haƙuri, bana son ki shiga damuwa ne" Barrister Habib ya ce "Hajiya, ina ga mu bi komai a hankali, Nabila menene watannin cikin, kuma kwana nawa da ɗaura musu aure, tun da an ce ai lokacin da ya saceta da ciki, ya ci ace zuwa yanzu ta haihu. Ramma tayi wiƙi-wiƙi da ido tana kuka. "Kiyi magana dan ubanki" Nabila ta ce "Yi mata a hankali, rahama meyafaru da wancan cikin?" Ramma ta kasa magana, ta cigaba da kallon mahaifiyarta da ta hasala. Nabila ta yi ta rarrashinta, amma taƙi magana fafur. Sumayya ta ce "Nabila, ku bi a hankali, zata yi magana, amma yanzu yakamata a rabu da ita, zuwa lokacin da zata samu nutsuwa tayi magana" Maman ramma ta ce "Har zuwa yaushe kenan, dan girman Allah ku yi mini rai a cire cikin nan" Barrister Habib ya ce "Haba Hajiya, baki bari an cire na farko ba sai wannan, dan Allah kar ki takura mata, ki ce sai ta yi miki bayani ko makamancin haka, ki yi haƙuri" Maman ramma ta dafe fuskarta tana hawaye, ta ce wannan wace irin wulaƙantacciyar rayuwa ce, an cutar da ni an wulaƙanta iyalina" Nabila ta ce "Mama jarrabawa ce, kowa da yadda Allah ya tsara masa, muddin muka taɓa cikin nan, zamu iya shiga matsala, tun da da izinin wakilinta ya aureta, babbar damuwar mu a nan shi ne, ayi masa hukuncin abin da ya aikata mata, amma ki yi haƙuri dan Allah" Nabila ta cigaba da rarrashin ta, tare da taimakon su sumayya. Sai da suka gama da mahaifiyar ramma sannan suka fito, suna ta jajanta lamarin, Sumayya ta ce zata tafi gida, Barrister Habib kuma zai mayar da Nabila, Nabila ta ce "Sumy, ki turo mini lambar mahaifin Viper please" Sumayya ta ce "Ok, amma ni haryanzu baki gaya mini tayaya ki samu alaƙa da matarsa ba" Nabila ta girgiza kai ta ce "Ai ni yanzu na daina dagewa lallai idan na faɗi abu sai an yadda da ni, lokaci zai warware komai" "Shikenan, ba zan matsa miki ba, zamu gani, amma Nabila nayi mamakin ganin Viper, lallai ya ci sunansa Viper, wallahi na zata zan ga wani karabutin mutum kawai, kalleshi masha Allah, lallai wannan su suke yin dabar gaske" Nabila ta ce "Malama ya daina daba fa, ki daina zancen dabar nan Please, ya tuba" Sumayya tayi murmushi ta ce "Allah ya baku haƙuri, sai mun yi magana" "Ok, bye" suka yi sallama. **** Sannu a hankali ta cigbaa da zaro kwalaban maganin tari, da satchet ɗin magungunan mura a ƙarƙashin gadonsa, kwalabe sun kusa ashirin, jikinta sai tsuma yake yi. Da kyar ta iya amsa sallamar da Shahida take yi a tsakar gida, ta fito jiki a sanyaye tamkar munafuka. "Mama ya dai? Na ganki kamar a tsorace meyake faruwa ne?" Alama ta yi wa shahida da hannu da ta shigo, ta ƙarasa cikin ɗakin Abba, ta nuna mata tulin kwalaben maganin tari masau hatsarin gaske. Shahida ta dafe kai ta ce "Mama kin gani ko? Na daɗe ina gaya miki amma kin ƙi yarda" Rahila ta ce "Duk laifin babanku ne, tun da ya kore shi daga kasuwa shi da Nazifi, ya rasa abin yi ya shiga wani hali, ni da nake ta fatan nayi masa aure" "Mama Abbu fa ba shi da laifi, yayi iya ƙoƙarin sa a kansa, ya zai zauna da su, suna cutarsa" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, na shiga uku ni Rahila" "Ina Amira ne?" Tamkar ta fashe da kuka ta ce "Amira yau kwananta biyu bata gidan nan, ban san in da take ba, na yi wa babanku ƙaryar tana gidan Yaya, Shahida na shiga uku" Jiki a sanyaye ta ce "Mama baki shiga uku ba, ni fa daga kotu nake, na kai Anwar ƙara ya sauwwaƙe mini, ba zan iya ba na gaji" A razane ta ce "Ya sauwwaƙe miki? Shahida baki da hankali, a wannan ƙadamin da ake ciki zaki kaso aurenki, ya ki ke so nayi, sai duniya tayi mini dariya?" "Mama, kin kasa gane in da na dosa, wai so ki ke sai na halaka ne, saboda kawai yana da kuɗi, nayi haƙuri fa iya haƙuri, ke fa uwata ce, haƙurina ya ƙare, Allah da zan iya tunkarar Abba, da sai na tunkare shi na sanar masa". "Shahida uban naki zaki tunkara da wannan maganar? Saboda baki da kumya?" Cikin tsiwa ta ce "Idan ba irin Amira ki ke so na zama ba ki ƙyale ni dan Allah" Rahila ta kwantar da murya ta ce "Ki rufa mini asiri Shahida, shi wannan ya fara shaye-shaye, waccan bin maza, shi Nazifi ya gudu kudu neman kuɗi, ban ma san a duniyar da yake ba, ke kaɗai ce a ɗakin aure nake jin daɗi, kar ki gurguɗe auren nan, ki ƙara tona mini asiri, ba ya ce miki yana neman magani ba? Baki san me Allah ya ɓoye a lamarin nan ba, ga tarin dukiya yana da ita, sai ki ga ke kin haihu da shi, ki haifi namiji, wannan dukiyar ta zama tamu" Ta kalli Rahila cikin takaici ta ce "Na haihu ta yaya, mama shekara uku fa, wane irin magani ya kasa nema a kan sauran matan da ya rabu da su? Ashe aurensa tara ni ce ta goma ya ɓoye mana, ga shaye-shaye ga cin mutunci har da duka wasu lokutan, wallahi ba za a kashe ni da raina ba, gara na auri talakan tulus in samu nutsuwa da kwanciyar hankali" Rahila ta ɗora hannu a ka, ta din ga kurma ihu, tana kukaz Shahida ko a jikinta, ta tashi ta shige ɗaki ta bar ta. *** Abin duniya duk ya damu liti, da yayi juyi ya ga babu ɗan mama sai yayi ta tsaki, da daddare ma kasa bacci yayi, sai tsaki yake yi. Walid ya ce "Sarkin gida" "Mai laya" Walid ya ce "Wai ya ne?" "Wallahi tunanin yaron nan nake yi, Allah ya sa ba suna can suna jibgarsa ba, ka san ba imani ne da su ba, kuma ga sauron wurin nan" Walid ya yi dariya ya ce "Allah liti, kai ne kake tunanin halin da ɗan mama yake ciki? Dama ka damu da shi har haka?" Liti yayi tsaki ya ce "Wallahi ban san ya aka yi ya shiga raina haka ba, ka san ya iya ladabin makirci, wallahi da ya dawo wurinmu, rashin Nura ya sanya nake yin sa" Viper ya yi gyaran murya ya ce "Ka yi haƙuri duk laifina ne, amma in sha Allah ba zai wulaƙanta ba zai fito" "Idan ma cewa kayi ba zai fito ba, ya tafi kenan dai-dai ne Ogana" Viper ya ce "Zai ma fito, ni kaina nayi mamakin yadda ya shiga raina, Allah sarki ɗan uwana Nura, Allah ya sanyaya makwancinsu da shi da mahaifiyata, da Sadik, da uban gidana dodo, da kuma matata a bar ƙaunata, da dukkanin wanda muka rasa" suka amsa masa da Amin. Liti dai bacci gagararsa yayi, sai tsaki ya din ga yi yana juyi. Gidan da Nabila take, aka gabatar mata da wata macen soja, a matsayin mamallakiyar gidan, ba ta gari ne ya sanya Nabila take zaune a gidan tare da masu aikinta. Nabila ta zata zata ga matar masifaffiya, kasancewar an ce soja ce, amma taga ba haka ba, tana da matuƙar kirki da sauƙin kai. Nabila ta din ga jujjuya lambar mahaifin Viper tana son ta kira, amma tana tsoron tijarar Viper, kasancewar ya gargaɗeta a kan haka, tana cikin tunanin, sai ga kiran Viper sai da ta kusa katsewa ta ɗaga ta ce  "SPY" "Idan ki ka sake suka ji abin da ki ke faɗa, zasu iya kashe ki, ban da ogana da ya zo wurnki da su Walid, babu wanda ya san kin san ni waye" "Yanzu har su Oga Walid basu sani ba" Ya ce "Mmmm" "Taɓ, sannu" "Yauwwa, ya rahama da mamanta? Ina son zuwa da gaske kamar yadda ki ka ce, na ga halin da suke ciki" Nabila ta ce "Akwai matsala, ciki ne fa da rahama" "What ciki ta yaya?" "Ya za ayi in sani, ciki dai, maman hankalinta ya tashi sosai da sosai, ta ce sai an zubar, wallahi na rasa yadda zan yi, gashi ta ƙi magana rahaman, muna son mu ji, kafin ya aureta cikin ya samu ko bayan ya aureta, amma na fi kyautata zaton bayan auren ta samu cikin, duk da bamu san meyafaru da wancan cikin ba da ta samu bayan ya mata fyaɗe" Viper ya haɗiye takaici, ya tsani ya ga an ci zarafin mace, mussaman mahaifiyar ramma da aka watsa mata yara gaba ɗaya babu wani wanda ta amfana an watsa rayuwar su, kuma abin mamakin uba da ɗa ne suka lalata mata rayuwar yara" "Bani adress ɗin in da suke zan je" yayi maganar a kausashe cikin damuwa. "Ka bari muje tare, ina ga idan rahaman ta ganmu tare, ta yi magana, kayi haƙuri na san ranka a ɓace yake, amma babu yadda muka iya da ƙaddara" yayi shiru yana huci. A raunane ta ce "Viper" "Mmmm" "Idan na mutu baka sadani da mahaifin jauhar ba, wanda nake kyautata zaton ina da alaƙa da ita ba, ba zan yafe maka ba" Dummm haka ya ji maganar Nabila ta dira a tsakiyar zuciyarsa. Viper "Kin san me ki ke faɗa kuwa? Ta ina ki ke da alaƙa da jauhar?" Tuni ta fara kuka ta ce "Abubuwa da yawa, na fara sarewa, tun kan na ganka nake mafarkinka, bayan ban sanka ba, ban taɓa ganinka ba, ina da ciwon Athma da take gada nayi daga mahaifiyata, ita ce take da ciwon, familyn su na Jalingo da yawansu, Asma ciwonsu ne, ita ma ka ce ciwonta ne. Akwai abubuwa da dama, ba zan ɓoye maka ba, Wallahi idan Allah ya karɓi rayuwata baka sada ni na mahaifina ba, ba zan yafe maka ba" ta ƙarasa maganar tare da kashe wayarta. *** Abba ya kalli Nasir ya ce "Nasiru, ya aka yi ne, an ce tun ɗazu ka ke nemana, na je wani wuri ne, ya aka yi?" "Na haɗu da Arfa" Abba ya ɗan yi sak, sannan ya ce "Tana lafiya" ya jinjina masa kai alamar eh. "Haryanzu ba ta yi regreting abin da tayi ba kenan, shirun da nayi mata da zuru duk bata saduda ba kenan?" "Babu alama, tare da ɗan daban suka je CID jiya" "What? Aka ce mini tana barrack wurin yarinyar nan Halima goza, ina sane da duk halin da take ciki ai" Nasir ya ce "Tare dai na gansu, tare da wasu 'yan daban ma, da sumayya" Abba ya yi shiru cikin takaici, wai 'yan daba. "Nabila ba ta da hankali, kuma bana tunanin zata yi shi, zan je na taho da ita, duk wadda za ayi sai dai ayi, basarwa kawai nake yi, amma hankalina yana kanta" "Abba" ya kalli Nasir. "A harabar wurin, ga abin da shi wanda take karewar ya bani"ya miƙawa Abba envelope. Cikin matsananciyar faɗuwar gaba, ya kalli Nasir ya ce "Hoton da ta kawo mini wancan karon dama ba Photoshop bane?, Har na fara tunanin waye ya gaya mata wani abu" "Abba ka san babu wanda ya isa yayi fatali da umarninka a cikin gidan nan" Muryar Abba har rawa take ya ce "Shi wannan ɗin waye a jikin hoton?" "Shi ne gayen, matarsa ce, ita ce ake shari'ar a kanta ai, ake zargin ya kasheta" A zabure Abba ya tashi tsaye jikinsa yana rawa ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, kuma Nabila saboda mahaukaciya ce, ta tsaya masa take fafutukar a wanke shi, Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Nasir kira mini Nabila a waya yanzun nan". Nasir ya ciro wayarsa daga aljihunsa, ya kira lambar Nabila, amma line busy. Ya ce "Abba line busy" Abba jikinsa na ta ɓari, ya ciro ta sa wayar, ya jefawa Nasir, ya ce "Kira ta maza" sai dai tun tana cewa line busy, aka ce wayar a kashe take. "Abba ta kashe wayar" "Nasiru, tashi ka ɗaukko mota mu tafi barrack" "Abba a daren nan, wajen gari ne wurin" "Ka tashi na ce!" Yayi maganar cikin tsawa. "Abba dan girman Allah kayi haƙuri, ka san ba zasu bari mu shiga yanzu ba, dan Allah ka yi haƙuri sai Allah ya kaimu gobe da wuri sai mu tafi. Anty da ta fara bacci, a bedroom ɗin Abba ta fito ta ce "Major lafiya kake ɗaga murya a daren nan?" Nasir ya ce "Bakomai" Har Abba zai bar falon, ya dawo ya nuna wa Nasir hoton ya ce "Waye wannan ɗin ne wai?" Nasir ya ce "Abba, na ce maka shi ne ɗan daban da nake nema, aka ce na kama, yarinyar jiki ya kashe.... Abba ya ɗaga masa hannu ya dakatar da shi, ya shige ɗaya ɗakin nasa ya kulle ƙofa. "Nasir meyake faruwa ne?" Anty ta sake tambayar Nasir cikin damuwa. "Bakomai"ya sake bata amsa a taƙaice ya fice. Abba ya ɗaukko wani hoto tun Black and white, da hoton wata matashiyar budurwa a jikin bukka ta buɗe haƙora tana dariya, aka yi mata hoton. Ya haɗa da hoton da Nasir ya bashi, gabansa ya tsananta faɗuwa ya ce "Anya ban tafka kuskure ba kuwa? Hukuncin da na yanke bai yi muni ba? Kana naka Allah ya na nasa. Innalillahi wa Innalillahi raji'un, na yanke hukunci cikin fushi, bayan shekaru Allah ya jujjuya ƙaddara yadda yake so, ki yafe mini mairamu" yayi maganar cikin matsanancin rauni. Kwana Abba yayi a zaune, yadda ya ga rana haka ya ga dare, cikin tashin hankali da rashin sanin abin yi, ya din ga jinjina girma da ƙudurar Ubangiji. *** Sojar nan sai mita take yi wa Nabila, ta ƙi sakin jiki ta karya. Ƙarfe bakwai da rabi, Viper ya je gidan, suka gaisa da Madam, ya ce "Nabila ta shirya, za su fita" Madam Goza ta ce "Ka karɓo permisson ne?" "Eh sun sani, wurin aiki zata je, muna ta shirin shiga court" Ta jinjina kai ta ce "Best of luck" Ya amsa da thank you. A wata haɗaɗiyar mota helux mai fentin sojoji, aka ɗauke su. Da ƙyar Nabila ta iya ce masa "Ina kwana" Shiru yayi bai amsa ba, ita ma ta ja bakinta ta tsuke. Gaba ɗaya fuskarta mamaye da damuwa, kamar ma ba ta samu isasshen bacci ba. "Meyasa ki ce ba zaki yafe ba, idan ban haɗaki da iyayen jauhar ba, Allah ya isa fa ki ka yi mini kenan" Cikin rauni ta ce "Ya ka ke so na yi, ka ƙi fahimta ta, Allah ke da yau da gobe, balle ka ce akwai lokacin da ka zaɓa, ka nuna mini iyayenta". Ya numfsa ya ce "Kalmar tayi mini nauyi sosai, kasa bacci nayi" ta yi masa shiru, tana kallon window tana share hawayenta. Ya kamo hannunta ɗaya, ta kalleshi da sauri, ta fara ƙoƙarin ƙwace hannunta. "Ki daina kuka, jauhar ɗina nake gani, kar nayi ɓarna dan Allah" "Cika ni, ni ba ita ba ce, ni maganin kukana Allah" Ko a jikinsa ya ce "Kar ki ce zaki yi kishi da ita, wahala zaki sha" Shiru ta sake yi masa, tana duba wayarta. Nasir ya turo mata message "Ki ɗaga wayata, zamu zo ni da Abba" kasje wayarta tayi, saboda a jikinta ta ji Nasir ƙarya yake yi. **** A rikice maman ramma ta tashi, ganin Nabila tare da Viper, ta nufe shi da sauri ta fashe da kuka. Riƙeta yayi, jikinsa a sanyaye yana tuno Nura guduma, ya ɗagota yana share mata hawaye ya ce "Mama, ki daina kuka dan Allah, na san ni mai laufi ne, rabona da ke na daɗe, amma ƙaddara ce ta janyo duk hakan". Cikin kuka ta ce "Murnar ganinka nake yi Aminu, ashe zan sake ganinka? Ni da Hajiya mun zo wurinka sau uku, tun daga ƙauye amma ba a bari mu ganka, Allah bai ƙaddara zaku sake ganawa da ita ba" Aminu ya ce "Allah sarki, ki yi haƙuri ke gashi Allah ya ƙaddara ganawarmu ai" yayi maganar yana zaunar da ita a kan kujera. Nabila ta gaisheta, ta amsa tana kallon Nabila tana kallon Viper, gashi an hanata magana. "Jauhar a ina ki ka gano shi? Ya aka yi ki ka san muna da alaƙa da shi?" Viper ya ce "Nabila ce wannan, ita ce lauyar da zata tsaya mini nima, kuma take ta ƙoƙari a kan shari'ar rahama. Komai da ake ciki tana gaya mini, ina son na zo na ganki na gaishe ki, amma kin san jami'an tsaro nemana suke yi, kuma ina tsoron ki yi mini kallon ɗan ta'adda da ya kashe matarsa" Cikin ɗaurewar kai ta ce "Wai ni fa na rikice, tayaya Jauhar ta koma Nabila kuma?" Viper ya ce "Zancen dogo ne, yanzu mu fara gamawa da batun rahama" yana maganar ramma ta fito cikin hijjabi. Mammaki ne ya kama shi, har ya tafi prison yarinya ce ƙarama sosai, amma yanzu ta zama wata uwar mata, tayi ƙiba, tayi haske sosai. Cikin matsanancin tsoro, ta gaida Viper, ita gaba ɗaya taoro yake bata tun lokacin da ta taɓa ganinsa a asibiti da kuma lokacin da ya zo gidansu" Viper ya yi mata alama da ta zo. Ta ƙarasa gefe kusa da Nabila ta zauna. "Maganar me ake so ki yi ki ka ƙi yi? Sai kin yi magana za a iya ƙwatar miki hakkinki" Jiki na rawa Ramma ta kalleshi, amma ta yi shiru. Tsura mata ido yayi ba tare da yayi magana ba, babu shiri ta fara bayani tiryan-tiryan. Nabila ta ce "Taɓɗijan, wannan case ɗin akwai sarƙaƙiya, cikin jikinta na halal ne ai" Maman ramma ta ce "Dan girman Allah ku taimake ni a zubar da cikin nan, yaron nan ba shi da tarbiyya ko kaɗan, babu ɗan da zai yi alfahari da shi a matsayin uba, ni dai bana buƙatar sa". Viper ya ce "Na goyi bayan haka, yakamata ta koma makaranta ne, ta fuskanci rayuwarta da ƙalubalen rayuwa" Ramma ta fashe da kuka, Nabila ta ce "A'a dan Allah ku yi haƙuri, laifi ne na kisan kai, ko kin yadda a zubar?" Tayi maganar tana kallon ramma. Ramma ta girgiza kai ta ce "Mama dan Allah ki yi haƙuri, nayi masa alƙawarin ko an kama shi, ba zan zubar da cikin ba, dan Allah ki bari na haihu, ya ce mini mutuwa ake yi idan aka zubar da ciki" tayi maganar cike da yarinta da wauta. Salati suka hau yi, Viper kawai ya jinjina kai. Ya tashi ya ƙarasa gaban Ramma, ta sake takurewa gabanta na tsananta faɗuwa. Ya ce "Kin san yayanki Nura ko da ya mutu?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Baban wannan mutumin da yayi raping ɗin ki, ya ci mutuncin ki, shi ne ya yi sanadiyar mutuwar sa, bayan ya yi masa fyaɗe ta wurin bayan gidansa, idan kin zaɓi ki rufa masa asiri ba zaki bayar da haɗin kai ayi abin da ya dace ba, ba kanki kawai ki ka cutar ba, har da marigayi ɗan uwanki" Toshe baki ramma tayi, tana bin Viper da kallo, jin maganar tasa kamar almara, sai yanzu wasu abubuwan suka din ga dawo mata. Nabila ta ce "Vi da ka sani baka gaya mata a haka ba" "Muddin aka tafi a haka, zata baki kunya a wurin Shari'a, alamu sun nuna zata iya ruf masa asiri" Ya kalli maman ya ce "Mama, zamu tafi, akwai uzururruka da zamu yi amma zan dawo, ki yi haƙuri, na san na fama mana wani ciwo mai wuyar warkewa. Ta jinjina masa kai ta ce "Gara da ka yi mata hakan, na gode Aminu, Allah ya kula da kai ya tsare mana kai. Kema Allah ya rufa miki asiri duniya da lahira". Tayi maganar tana kallon Nabila, bakinta fal maganganu, da tambayoyi, sai dai gargaɗin da aka yi mata ya hanata tambayar, amma har a wannan lokacin zuciyarta na bugawa cikin tsananin tashin hankali da mamaki, a duk lokacin da ta ga Nabila, mussaman a yanzu da ta gansu tare da Al'amin, kuma ya ce mata ba Jauhar ba ce. **** Abdul yana tare da su Salim, ya sha ya bugu yayi mankas, dan abin da yake yi kenan ya samu sassauci, gaba ɗaya nema yake ya haukace saboda rashin sanin in da ramma take. Salim ya miƙe yana ƙoƙarin kama shi su tafi, kawai suka ga an kewaye su, wasu mutane sanye da kaya personal. Ba su yi musu wani dogon jawabi ba, suka kama su gaba ɗaya suka tafi da su. Indabo yana Abuja, zuwa kano ya gagare shi, duk da zaman Abujan ba daɗi yake yi masa ba, kotu ta yi seazing ɗin passport ɗin sa, babu damar fita ƙasashen waje, har sai an kammala bincike, kwamiti biyun da aka kafa, na binciken kuɗaɗen da aka karkatar, duk sunansa ya fito a ciki, ga kuma tuhuma daga ɓangaren EFCC. Gefe guda kuma, a Kano mutanen yankinsa na shirin yin abin da ba a taɓa yi ba a Nigeria, shi ne yi masa kiranye, ya dawo daga Abuja ba su gamsu da wakilcin da yake yi musu ba, ya rasa wane tunani yakamata ya yi, wace mafitar yakamata ya fara nema. Ana tsaka da haka aka kira shi a waya, aka sanar da shi an kama Abdul, ba a ma san wace police station ɗin aka kai shi ba, abokansa ne suka sanar da kama shi. Hakan ya ƙara gigita shi, da tayar masa da hankali, ya fara shirin tahowa Kano. **** An so a kai ruwa rana kafin a bawa Abba damar ganin Nabila, sai dai kasancewar shi ma retired solder ne, aka bashi damar hakan. Sai dai suka tarar da Nabila bata nan. Gaba ɗaya Abba ya rikice, ya din ga faɗa ya ce "Shi ba haka aka yi masa bayani ba, an ce za a riƙe masa 'ya ƙarƙashin kulawar hukuma, dan me zai zo ace bata nan" "Sir, bawa yarinyar nan kariya baya nufin mu yi ta ɓoyeta, akwai ayyukanta da take gabatarwa na aikinta. Sun fita an yi mata rakiya zuwa wurin gudanar da aikinta, rayuwarta na cikin haɗari ne". "Rayuwarta na cikin haɗari, sai a kauwwameta a cikin barrack ma tukuna, ba 'yan sanda ne yakamata su bata kariyar ba ma, menene haɗinta da ku kuma?" "Akwai dalili mai girma, da ba zamu iya gaya maka ba sir" Ya sake kallon Nasir, ya ce "Kira mini ita" Nasir ya sake kiran wayar Nabila, wayar na hannun Viper, Nabila kuma ta shiga cikin ma'aikatar Shari'a tare da barrister Habib. Ɗaga wayar ya yi ya saka a kunnensa "Arfa, tun jiya ake kiranki a waya kin ƙi ɗagawa, Abba yana son ganinki lallai kina ina yanzu?" Kai tsaye Viper ya ce "Na tafi kaita wurin mahaifinta" A sukwane Abba ya kalle shi, saboda a hansfree wayar take, ya ce "Waye wannan?" Abba ya karɓe wayar jikinsa na tsuma ya ce "Who are you, waye ya baka wannan damar? Kana ina? Ina 'ya ta?" Cikin girmamawa Viper ya ce "Am sorry sir, wannan alƙawari ne da nayi wa Nabila, a matsayin hakkinta na aikin da tayi mini. Na baku damar sanar da ita komai, saboda ban san dalilinku ba, amma ka bata damar ta je ta nemi mahaifinta. Nima ina buƙatar sanin, menene alaƙarta da matata". "Stop it, kar ka kuskura ka kai Nabila wurin wannan mutumin" "Am very sorry sir" Cikin tashin hankali Abba ya ce "Ku san yadda zaku yi, ku dakatar da mutumin nan, ku gaya mini in da yake ya dawo mini da ya ta, bamu yi da ku ku bari tana yawo da yan daba a gari ba. Viper ya tsurawa Nabila ido, tana nufo motar, ta ƙaraso ta buɗe motar tana yi masa magana. "Lafiya kake kallona haka?" "Shigo muje wani wuri, zamu ɗauki su Walid mu tafi" Jiki a sanyaye ta ce "Ina?" "Zaki gani" ta ce "To" Ta shiga motar ta zauna, hakanan sai ta ji jikinta yayi sanyi, kamar an zare mata laka. A ransa ya ce "Yau komai zai zo ƙarshe in sha Allah" Indabo ne a hukumar yansandan farin kaya, kamar zararre, yana ta masifa da tambayar ba'asin menene dalilin da ya sanya aka kama masa ɗa. Da ƙyar aka lallaɓe shi ya zauna, "Honorable, ana zargin ɗanka da aikata laifin fyaɗe, tare da ɓoye yarinya ba da sahalewar iyayenta ba, sannan bayan mun kama shi, mun same shi da miyagun ƙwayoyi ciki har da waɗanda aka haramta shigowa da su ƙasar nan, wanda ta'amalli da su babban laifi ne" "Wannan duk ƙage ne da yarfe da son ɓata mini suna da siyasata, sharri aka yi masa, bai aikata ba, ku sakar mini ɗa kawai" "Distinguish senator, kai babban mutum ne a ƙasar nan, kar mu yi ta jayayya da kai dan Allah. Duk wasu shaidu da hujjoji da ake buƙata muna da su, shi ya aikata laifin, dan haka kotu ce take da damar wanke shi ko kuma hukunta shi, kayi haƙuri aikinmu muke yi. Ayshercool 08081012143 83 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 "Ban gane aikinku ku ke yi ba, wane irin aiki ne babu evidence, kawai ku kama mutum ku rufe shi?" "Distinguish, na sanar maka yaron nan fa muna da evidence a kansa, ciki har da videon da CCTV camera ta ɗauka, lokacin da yaje gidan, dan haka musu ba naka bane ba. Babbar shawarar da zan baka bai wuce ka je ka nema masa manyan lauyoyi da zasu tsaya masa ba" gaba ɗaya jikin Indabo yayi sanyi ƙalau, cikin mamaki da tsantsar tashin hankali ya ce "Ka ce kana da videonsa lokacin da ya shiga gidan?" "Ƙwarai kuwa, da cikakkiyar hujja da aka bamu muka kama shi, kuma wadda ya aikatawa abin, tana tare da hukuma, kuma ta tabattar da hakan da bakinta, dan haka zamu gurfanar da shi a gaban kotu kamar yadda kotun ta buƙata" Indabo ya cire hular kansa da ya ji gumi na barazanar ture ta daga kansa, ya shafi shimfiɗaɗen sanƙon da gwagwarmaya ta raba tsakanin gashin kansa, yana sauke numfashi yayin da bugun zuciyar sa ke ƙara hauhawa tamkar ta tsaga ƙirjinsa ta fito. "Ina Abdul ɗin yake?" Jami'in ya ce "Mu je na kai ka ka ganshi" yayi wa indabo jagora, har zuwa in da aka rufe Abdul, yana ta tangaɗi, sai da ba iya mayen yake yi ba, har da magagin ciwon da yake sakaɗarsa, sai dai mayen da yake yi ya hana shi gane takamaimai abin da yake danunsa. "Abdul yasar" Indabo ya kira sunansa cikin tashin hankali, ganin a wurin da aka ajiye shi, ɗan ƙut a takure, duk wurin babu tsafta, har gari prison ɗin da ɗan uwansa yake a ƙasar waje, a kan wurin nan da aka ajiye Abdul. Abdul na jin muryar Indabo ya taso, cikin maye ya ce "Daddy dan Allah ka fito mini da ramma, kar na mutu ban ganta ba, ban ga ɗa na ba, akwai ɗa na a cikin ta, dan Allah ka yi mini rai, ka dawo mini da ita rahama rayuwata ce" "Dalla rufe mini baki, soko bita zaizai yarinyar da ta tona maka asiri, ta tabattar da kai ka yi mata fyaɗe ka ke nema, saboda baka da hankali, ita tayi silar shigarka wannan halin da ka ke ciki" Abdul ya ɗaga idanunsa da kyar, ya ce "Rahaman? Ta fara so na fa, kai wannan zance ne, rahama ba zata taɓa yin haka ba, kai ka saceta kawai ka fito da ita, tun kan na faɗi komai, a bani mata ta kawai mu bar garin nan, kan na fasa ƙwai mai wari" yayi maganar yana zamewa a hankali ya faɗi ƙasa, saboda ciwon cikin da ya murɗe shi. Indabo ya ce "Abdul, kai Abdul anya yaron nan lafiyarsa ƙalau ku fito da shi a san abin yi". "Lafiyarsa ƙalau a cikin maye yake, zai miƙe ya ware ne, kar ka damu" Indabo ya ja jami'in suka koma gefe, ya ce "Officer babu yadda za ayi ne? Zan bayar da ko nawa ne, ku sakar mini shi dan Allah" "Am so sorry sir, hakan ba zai taɓa yiwuwa ba, ana sane da duk wani motsinmu, kayi haƙuri lauyoyin dai yakamata ka ɗaukar masa" Indabo yayi shiru bai sake cewa komai ba, ya fice ya bar wurin. Yana komawa gida mahaifiyar Abdul ta tare shi cikin damuwa da tashin hankali ta ce "Yaya ake ciki? Ina Abdul ɗin yake?" Ya girgiza mata kai ya ce "Da gaske an kama shi, wannan karon bana tunanin kuɗi da sanayya za su yi amfani, kuma wannan duk munafuncin kankarofi ne, da ni yake zancen" Hannu ta ɗora a ka, ta fara kurma ihu "Na shiga uku naga ta kaina, shikenan gaba ɗaya yaran rayuwarsu ta tarwatse, babu wanda zan mora? Wannan wane irin abu ne?" Indabo ya ce "Kiyi haƙuri mana, ai matsalar Abdul da sauƙi, nan gida Nigeria ne, komai zai zo da sauƙi da yardar Allah, ki yi haƙuri ki daina wannan kukan" da kyar ya din ga rarrashinta, gaba ɗaya hankalinta ya tashi. *** Ramma na kwance, jikinta ya ɗauki zafi, ga tarin damuwa, mama sai faɗa take yi mata, tana kiranta mara hankali, saboda furucin da tayi, a kan kar a zubar mata da ciki. Mama ta cigaba da jaddada mata abin da baban Abdul ya yi wa Nura tana kuka, wanda hakan ba ƙaramin taɓa zuciyar ramma yake yi ba. Haka nan ta ji ta kasa hukunta Abdul da laifin da babansa ya aikata, ita burinta ɗaya a hukunta shi a kan ci mata zarafi da yayi, shi ma ƙasan zuciyarta tana fatan a sassauta masa, mussaman ta ɓangaren alkhairin da ya yi wa garinsu, da kuma yafiyarta da ya din ga nema babu yau babu gobe. Ta din ga tunanin ko yana cikin wani hali yanzu oho. Sai dai duk da haka, abin da aka yi wa yayan nata ya daketa, ya taɓa zuciyarta nesa ba kusa ba. *** Gaba ɗaya Abba ya tashi hankalin sojojin nan, a kan lallai su nemo masa yar sa a take, ba sai bayan wani lokaci ba. Lallai su kir wannan ɗan daban, ya dawo masa da yarinyar sa. Nasir kuwa gefe ya koma yayi shiru yana nazari tare da takaicin daɗewar da aka yi Nabila tana raina masa hankali. Ya kama liti, aka sake shi, ya yi target ɗin Walid, kwatsam ya daina zuwa wurin saida shayi, yayi target ɗin ɗan mama shi ma ya suɓuce masa, yanzu ya ƙara tabattar da Nabila shigo-shigo babu zurfi tayi masa, ta din ga rusa masa aiki, ashe mama son sa take yi, da take ta ankarar da shi a kan Nabila, amma ya kasa ganewa. Sai dai duk da haka, ya kasa tsayawa ya ji haushinta sosai, sai haushin Viper. Ya tsane shi ta kowace fuska, saboda yadda yake tozarta masa careersa ta aiki, kuma ya yi imani da cewa shi ne yake ziga Nabila yake yaudararta da wannan hotunan da daɗin baki, take kare shi, saboda ya ga yana da makamin yin hakan. Nabila a hanya suka ɗauki liti da kuma Walid, Nabila ta ce "Oga walid ina kwana?" "Lafiya ƙalau, ya aiki?" "Alhamdilillah" Viper ya kalli yadda ba su kula juna da ita da liti ba, yayi gyaran murya ya ce "Kin yi wa Abdallah fa laifi" Ta ce "Waye hakan?" Ya ce "Liti mana" "Nayi masa me?" Ya ce "Kin saka an kama masa ɗan mama, kasa bacci yayi jiya, gashi dama shi ma kin taɓa sakawa an kama shi. Kin saka sa da suka je CID suka kai masa abinci, suka zo in da muka haɗu" Cikin tsiwa Nabila ta ce "Ni na matsi bakin ɗan maman na ce yayi magana, to ya fashe ya huta mana" "Viper ka daina haɗa ni da yarinyar nan, zan iya karairayata ba ta da kunya" Viper ya ce "Easy mutumina, a din ga yi wa 'yar madara kara mana" "Dan Allah ka daina haɗata da waliyiyyar baiwa, babu haɗi kashi da fura". "Waye kashin waye furar?" Daga gaban motar ya waiwayo a fusace ya ce "Ke ce kashin, ke kin isa ma na haɗa ki da jauhar, mutuniyar kirki, yar aljanna, ai wallahi an cuci yar madara idan na ana haɗata da ke, shi kansa Vipern ƙular da ni yake yi, yadda yake kula ki. Kamar nayi muku dukan tsiya, ai wallahi an ci amanar 'yar madara. Kuma ba zai aure ki ba, sai dai ki je can ki auri wannan suɗaɗɗen yayan naki, tun da an ce sonki yake yi. Yar madara an yi an gama, kuma ba za a sake ba wallahi" "Aikuwa sai dai baƙin ciki ya kasheka, Allah a saki Anas, a kama ka" Walid ya ce "Dan Allah liti kayi haƙuri, kai a duniya kamar kuturu saboda naci da nanata magana" "Kaga ka ƙyaleni na yi mita ta, ina raye ana cin amanar yar madara mai bani taliya da cincin ga ladabi sama da ƙasa, kawai sai wasu abubuwa yake yi yana sakarwa wannan fuska. Ni wallahi idan aka dame ni, na fasa kai ku wurin, ku je ku nemi wurin da kanku" Walid ya ce "Allah ya baka haƙuri, Allah ya huci zuciyar ka" "Eh naji Amin, yarinya sai taurin kai da nacin tsiya, itakaɗai a cikin maza, zaratan 'yan daba, kamar ba mace ba. Yar madara da ko haɗa hanya ba ta iya yi da maza" "Ni yakamata ka gaya wa haka Abdallah ba Nabila ba, idan ka ci zarafinta kamar juhar ka yi wa, ni kuma taɓa jauhar taɓa ni ne kai tsaye yakamata ka kiyaye" Liti ya ce "Easy maza, tuba nake ba zan sake ba in sha Allah" Nabila kuwa tuni ta fara kuka, ta ji haushin maganganun da liti ya gaya mata, Walid ya din ga bata haƙuri, liti yayi musu banza. Viper sai ya tsinci kansa da kasa bata haƙuri, maganganun liti suka yi tasiri a zuciyarsa, ya ga tamkar cin amanar jauhar yake yi. Sai dai kuma yana tsananin tausayin Nabila, so take yi masa da gaske ba na wasa ba. Wayarsa ce ta fara ringing, ya ciro ya ɗaga. "Viper kana ina ne?" "Na je wani wuri ne" "Maza maza ka dawo, idan ka san kana tare da yarinyar nan barrister ka dawo da ita, mahaufinta ya zo yana ɗaga mana hankali" Viper ya ce "Muna tare, amma mun yi nisa gaskiya, zan turo muku, address ɗin da muke, a bashi" "Viper" sojan ya kira sunansa da ƙarfi. "Am sorry sir, am ready to face the consequences of my actions, ba zan iya dawowa yanzu ba" ya ajiye wayar. Nabila ba ta kula shi ba, balle ta ji da wa yake waya. Sai dai yana gama wayar, ta ta wayar ma ta fara ringing, ya miƙa mata, ta ɗaga. Cikin girmamawa suka gaisa da mai kiran wayar ta ce "Eh muna tare bari na bashi" Ta miƙa wa Viper wayar. Ya kalleta yana jiran jin ba'asin waye. "Ka karɓa mana" tayi maganar tana kallonsa. Ya saka hannu ya karɓa, ya saka a kunnensa ya ce "Salamu alaikum" Cikin matsananciyar rawar murya ya ce "Aminu, Al'amin ni ne, Al'amin ka yi mini magana dan Allah" sauke wayar yayi, yana yi wa Nabila wani irin kallo, take ta sha jinin jikinta, wani fitsarin tsoro ya cika mata mara, wani irin kallo yake yi mata mai cike da tuhuma da kuma tambayoyi. "Ban gargaɗe ki a kan abin da ki ka aikata ba?" Walid ya ce "Menene kuma?" "Dan me, meyasa ki ke da taurin kai, mutumin da ya ce baya buƙatar ɗan ta'adda a cikin rayuwarsa zaki haɗa ni da shi, ban gargaɗe ki ba?" A take Walid ya fuskanci in da zancen ya dosa. "Ba magana nake yi miki ba" Viper ya yi mata tsawa cikin maɗaukakiyar murya. Fashewa tayi da matsanancin kuka, ta takure a jikin ƙofra motar tana kiran suna. Abba cikin matsanancin razani da tashin hankali. Ƙoƙarin buɗe ƙofar  ta din ga yi, dan gara ta buɗe ta dungura tayi waje, da wannan tashin hankalin da yake yi mata. "Viper zata fita fa ka hanata" liti yayi maganar cikin tashin hankali. Sojan da yake jan su, ko a jikinsa ko kallonsu bai yi ba, balle ya saka musu baki. Allah ya sa an yi locking motar. "Hey stop here, let's reverse, take us back to barrack" "A'a ba zamu koma ba, abin da zai saka mu koma, ka sake mayar da mu baya, abin da tayi dai-dai ne, ka yi haƙuri kawai malam". "Mai laya, dan me zata nemi lambar mahaifina ta haɗa ni da shi, kin je kin haɗu da shi kenan ko?" Ta girgiza kai cikin tsoro tana kuka. Walid ya ce "Mai zamani, dan Allah ka nutsu, ka yi haƙuri, mutumin nan zai yi reverse fa, ka hana shi dan Allah da kyar ya shawo kan Viper, suka cigaba da tafiya. Abbu kuwa miƙewa yayi a razane, yana ta tsuma, yana sake kiran layin Nabila, amma ya ji an kashe wayar. Bai gaji ba ya cigaba da trying, amma shiru ba ta shiga, Ihun rahila ya jiyo a waje, ya fito da saurin gaske, ya tarar da Abba a buge, yana ta ball da ita a tsakar gida. Shahida ta maƙale a bango, sai ihu take yi tana neman ɗauki, da sauri Abbu ya ƙaraso, ya hankaɗe Abba gefe, sai dai tuni Rahila ta riga ta suma, saboda yadda ya din ga dukanta da ƙafarsa. Abbu ya ce "kai yanzu kana son ka gama da duniya lafiya, uwar taka ka ke duka saboda lalacewa?" Shahida ta ce "Wai kayansa ta kwashe masa, shi ne yake daketa" Kururuwar da maƙwabta suka jiyo, tuni suka fara shigowa, aka kwasheta aka tafi da ita Asibiti. *** Tafiya suke Nasir na ta fafara gudu, amma Abba mita yake yi, gani yake kamar Nasir baya sauri. Yayi shiru ya kashingiɗa, ya tafi tunani. JALINGON JIHAR TARABA. can cikin wani jeji, da ke ƙarƙashin ƙauyen gamyel. Ƙatuwar harabar gida ce, mai da sashe sashe ne a cikin gidan. Mai ɗauke da bukkoki. Akwai tarin turaku da ke ɗaure da shanu, a wasu sassa na gidan, daga wani sashe na gidan, matashiyar yarinye ce, 'yar shekara goma sha biyu, take surfa gero, ɗaya ɓangaren kuma wata matashiyar mace ce take iza wuta. Cikin harshen fulatanci ta ce "Chubaɗo, kina ganin har na gama tuwon nan, mu yi aikin furar nan da daddare?" Matashiyar yarinyar da take fara tas, da siririn billenta na fulani, ta ce "Eh mana, bari ma ki ga na ƙara sauri" sai kuma ta ɗan yi jimm ta ce "Dada, kamar kukan karsana nake ji, ko dai haihuwa za ta yi, bari na je na ga meyafaru" "Kul kar ki kuskura, kin san baffanki ya hanaki shiga turken shanu ko? Sai kin je makarai sun sake make ki a turken nan ko? Hanzarta ki gama, na san idan Habibu na nan, zai je ya duba". Ta cigaba da dakan geron, sallamar da aka yi ya sanya duk suka tsaya suna amsawa. Chubaɗo ta risuna ta ce "Baffa sannu da zuwa" "Yauwwa chubaɗo, aiki ake yi ne?" "Eh baffa" Ya ce "Sannu, ramata sannu da aiki" Matar ta ce "Yauwwa, sannu da zuwa" tayi maganar tana ƙoƙarin ɗaukko tabarma ta shimfiɗa masa. Yasar da taɓaryar hannunta tayi, ta fyalla waje da gudu, jin an kira sunan maitama a wajen. Tana fitowa, maitama ya saki akwatin hannunsa, ya ƙarasa ya rungumeta yana murmushi. Cak yaran da suke murnar ganinsa suka tsaya, ba su ba har da manyan da suke wurin, ganin abin kunyar da jibo ya aikata wato maitama. Ita kanta Chubaɗo sai ta ga abun wani iri, tayi sukuri da kai tana sunkuyar wa. Ya ce "Masha Allah, mairamu kin girma, ya ki ke" "Lafiya ƙalau hamma, ya birni?" "Birni Lafiya ƙalau tana gaishe ki"  ta ɗauki jakarsa ɗaya, shi ma ya ɗauki ɗaya, ya riƙe hannunta suka shiga gida. Baffa da yake shan fura, ya ɗago ya kalle su, ya mayar da kansa ya sunkuyar ya cigaba da shan fura. Jibo ya ƙarasa gaban baffa, ya durƙusa ya ce "Sannu Baffa na dawo" Baffa ya ce "Sannu" "Yauwwa" Ramata ta ce "Jibo sannu da zuwa" Ya ce "Yauwwa sannu" Chubaɗo ta shiga ɗaki ta shimfiɗa masa tabarma, ta ce "Ka zauna, bari na sake gyara maka ɗakinka, nayi ta mafarkinka, ashe ka kusa dawowa" yayi murmushi ya zauna, ta ɗebo masa ruwan randa, ta kawo masa, ta buɗe bukkarsa da shekara guda kenan, rabonsa da ita tana sake gyara masa. Babu wanda ya kuma kula shi, shi kuma ko a jikinsa, ya cigaba da hira da chubaɗo. Ta ɗauki ƙoƙo, ta tafi gidansu Habibu, da kanta ta shiga tsakanin shanu, ta tatso masa madara, mai ɗumi ta kawo masa, sai rawar kai take yi. Baffa yana fita aka sanar da shi abin kunyar da jibo ya tafka, na rungume chubaɗo. Hakan ba ƙaramin ƙona wa Baffa rai yayi ba, ya zubar masa da ɗan ragowar mutuncin daga dawowarsa, bayan wanda ya zubar masa a baya, yazo ya fara gwada yahudanci da baƙar ɗabi'ar da ya koyo. A fusace ya dawo gida, ya sake tarar da Jibo, yana ta hira da chubaɗo kamar wata sa'arsa. Yana yi mata tambayoyi a kan abubuwan da ya koya mata a baya, dangane da karatun boko da na addini, cikin ikon Allah bata manta ba, har sunanta da nasa, da haɗa baƙi duk bata manta ba. Sosai yake murna, kan ya jiyo muryar Baffa yana faɗa "Maitama, dama abin da ka je ka aikata kenan daga dawowarka, saboda yahudanci a gaban mutane ka rimbaci chubaɗo, saboda rashin mutunci" Jibo ya ce "Baffa chubaɗo fa ƙanwata ce ciki ɗaya, shekara guda rabona da ita, menene laifi a cikin hakan? Kuma naga ai ba wani girma ne da ita ba" "Zaka rufe mini baki, ko sai na rushe maka kai da sandar nan? Tashi kema daga kusa da shi, kana naɗa miki duka. Ka tashi mu je arɗo yana son ganinka yanzun nan, har labarin zuwanka da abin da aikata ya je masa. Kalle ka har ka fara tsufa, sa'aninka duk sun yi aure, sun kusa ma fara aurar da 'ya'ya kai kuma kana nan kana gararanba, kana shashanci" Jibo ko a jikinsa, ya ce "Nima dawowata yanzu har da maganar auren na dawo" "A ina zaka yi auren?" "A can in da nake ne" Baffa ya ce "To bayahudiyar zaka aura kenan, masu bawali a tsaye, to sai su yi maka waliccin auren, tashi mu tafi" tashi yayi ya bi baffa, ko da suka je fadar arɗo, tuni wasu manya a rigar sun taru suna jiran su. Aka hau jibo da faɗa, da jaddada kiransa da bayahude, kuma suka ce lallai ya tattara ya bar musu gari, kamar yadda aka yi yarjejeniya da shi da farko. Jibo ya gyara zamansa ya ce "Idan har kuna son na bar garin nan, sai dai ku bani mairamu chubaɗo, na tafi da ita, dan ba zan je na rayu nikaɗai ba alhalin ina da 'yar uwa ba, tun da ku kun sallama ni" "Babu wanda zai baka chubaɗo, kuma sai ka bar rigar nan, ai duk zuwa muna gaya maka, bama buƙatar ka tun da abin da ka zaɓawa rayuwarka daban" Ya ce "To shikenan, amma ku sani duk ƙasar nan babu wanda ya bawa wani ikon ya kori wani, muddin ba zaku bani chubaɗo ba, ku bar ni na din ga zuwa ina ganinta, idan kuma kun ƙi, kun san ƙasa nake yi wa aiki, za a aiko yahudawa kuma su kore ku, su kwashe shanunku" sai kuma duk suka yi saroro. Ya ce "Eh idan mun tashi zuwa kiwo, babu wanda yake hanamu shiga duk in da muke so da shanu, muyi kiwo, saboda yan ƙasa ne mu, amma idan ku ka ce zaku kore ni, to fa kuma za a kore ku daga rigar nan, kuma a ƙwace muku shanu". Gaba ɗaya sai suka sha jinin jikinsu, sai kuma suka koma rarrashin sa da neman sulhu. Maitama wanda suke kira da jibo, cikakken sunansa shi ne Yusuf, mahaifiyar su Allah ya yi mata rasuwa, a ƙalla ta haifi yara tara amma duk mutuwa suke yi, shi ne na huɗu, har an fitar da ran zata sake haihuwa, ta samu ciki ta haifi mairamu ake ce mata chubaɗo. Kowa ya ɗauki son duniya ya ɗorawa chubaɗo, mussaman ma shi. A can yawon kiwon shanu, ya faɗa wani ƙauye, ya tarar ana makaranta, turawa na koyar da yaran garin karatun boko. Abin ya ƙayatar da shi, ya fara shiga cikinsu, ya shiga cikin ɗalibai, kullum ya fito kiwo, sai ya je ƙauyen nan, komai kyauta ake ba su, da kayan rubutu da karatu. Gashi da ƙwazo, ya shafe wata shida yana zuwa ba a gane ba a gida, daga bisani wani a rigarsu ya gano shi, ya je ya faɗa. Ai tamkar za a cinye shi, aka ce kiwon ma ya daina zuwa gaba ɗaya. Baffa ya koma fita da dabbobin da kansa, sai dai yana ficewa, shi ma maitama yake saka ƙafarsa ya fita, ba boko ba har da karatun allo yake koya a garin. Baffa duk son sa da yara, sai da ya saka aka zane masa maitama, amma washegari ya gudu ya koma can ƙauyen ma gaba ɗaya. Yake kwana a masallaci, abin da zai ci ba wahala yake ba shi ba, kullum gidan mai garin ana bayar da abinci sau uku a rana. Innarsu babu irin nasihar da ba ta yi masa ba, da rarrashi, amma yaƙi. Hnakali ya tashi rashin ganin maitama, aka wakilta ƙarti suka tafi ɗaya garin,arɗo ya ce a ɗoro masa Jibo a ka a dawo masa da shi. Sai dai can garin suka hana kama Jibo, abu ya nemi ya zama rigima da fitina, sai da aka shirya zama na musamman tsakanin malaman dagacin ƙauyen, da ƴan rigar su jibo, a kan a samu fahimtar juna, su bar Jibo yayi karatu, su ma idan suna buƙata zasu iya kawo wasu yaran, a cigaba da yi musu karatu, amma suka ƙi suka ce ba sa son yahudanci. Abu sai da jami'an tsaro suka shiga, suka ce sai Jibo yayi karatu, ba tare da an cigaba da tsangwamar sa ba. Da kyar aka samu masalaha, sai dai can a riga suka ce, sai dai ya bar musu rigar su, babar sa ta din ga kuka tana yi musu magiyar kar su korar mata ɗa. Idan bai ga dama ba, idan ya tafi sai juma'a yake dawowa, kan ya dawo innarsu ta ɗan tanadar masa busashshiyar fura, man shanu, nono, ta ce ya tafi da su, kar ya ji yunwa, haka kurum ta ji ita dai tana son abin da yake yi. Ta fuskanci ƙalubale sosai da sosai, ana cewa ita take goya masa baya, duk lokacin da ya zo, idan zai tafi sai chubaɗo tayi ta kuka saboda sun shaƙu. Tana da shekaru huɗu, haka zai zauna da ita, yana koya mata idan baffa ya ƙyalla ido ya ganshi, ya ɗauke chubaɗo yayi ta yi masa masifar kar ya lalata masa yarinya shi dai ya je ya ƙarata. A haka aka zaɓi ɗalibai har da maitama, aka ce za a kai su makarantar kwana. Nan ma an sha gwagwarmaya, kan maitama ya tafi. Chubaɗo na da shekaru shida, Allah ya yi wa mahaifiyar su rasuwa, maitama yana can makaranta. Da ya zo hutu ya sha kuka, ya shiga tashin hankali da kiɗima mai yawan gaske. Da aka nutsa, suka sake ce masa sai dai ya zaɓa, ko boko ko ya dawo yayi aure, amma ya ce boko, suka ce to ya bar musu riga. Bai damu ba, bai kuma daina zuwan ba. Baffa ya auri ramata, ta riƙe mairamu hannu bibbiyu kamar ita ta haife ta. Sai dai tun tana ƙarama, take fama da matsalar numfashi, sai dai ko maganar asibiti ba ayi, sai dai ayi ta banka mata hayaƙi, wai iskokai ne, cike da jahilci. Ga kuma matsalar iskokai da take fama da su. Maitama ya ɗauke ta, ya kaita asibiti babu wanda ya sani, likitoci suka tabattar da athma ce da ita, wanda irin ciwon ne ya kashe mahaifiyar su. Sai da aka kusa ƙaramin yaƙi a zuriyar, saboda kai mairmu Asibiti da yayi. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, maitama ya yi degree, ya tafi aikin soja, amma duk sunansa Bayahude a wurin mutanen rigar. A yanzun ma haka suka ƙyale shi, bayan yi musu barazanar saka yahudawa su ƙwace musu shanu su kore su daga riga. Har magana yake yi wa mairamu da turanci, kuma tana iya gane wani abun. Ya fara kashe bakinsu, bayan da ya fara basu 'yar shinkafa kyauta. Lokacin aurensa da kyar suka je masa walicci, sai dai da suka ga birni sun rikice da yawa, ya so a bashi mairamu amma fafur suka hana shi. Shekaru suka cigaba da ja, chubaɗo na da shekaru goma sha uku a duniya, tsantsar kyawunta, ya fara baiyyana, samarin ƙauyen sun fara kawo hari, saboda kyakywar gaske ce, sai dai da yawa suna tsoron larurarta ta matsalar numfashi da suke cewa aljanu ce. Duk lokacin da Maitama ya zo garin, sai ya kawo mata kayan sawa, na kwalliya, wanda babu wata yarinya da ta taɓa amfani da su a rigar. Ya kan bugi cikinta duk wanda ya ji ya nuna yana sonta, sai ya je yayi masa barazanar saka yahudawa su kama shi, su mayar da shi ƙarfe. Ya kan kawo mata litattafai, ya sayo mata radio, ya gaya mata lokutan da ake gabatar da wasu shirye-shirye a radio na yara. Watarana da ta zama ranar mabuɗin sada chubaɗo da ƙaddararta, ta bi 'yan matasan matan da suke fita can bakin hanya sayar da nono, domin ta je ta ga motoci, ta fita da shanu, ta fake da haka, dan Baffa baya barinta ta je ko ina..... Ayshercool 08081012143 84 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Fitar ta yi wa mairamu daɗi sosai da sosai, dan ko kiwo zata fita, ba ta yi hanyar barin garin, balle ta fito bakin hanya. Suna zazzaune, shanunta na gefe na kiwo, sai nishaɗi take ji, tana ƙissima ta nan hanyar hammanta yake wucewa, idan zai zo riga, ko kuma ya tafi. Yayi mata alƙawarin komai daɗewa zai zo ya ɗauketa daga riga, ya tafi da ita can in da yake, ita ma ta ga gari, amma ba zata ji daɗin tafiya ta bar baffa da dada ba. Gashi rashin jituwar hamman da baffa baya yi mata daɗi, sai dai tana fatan barin rigar, tana son tayi karatu irin na hammanta, babban abin da yake ƙara burgeta da yi mata daɗi, shi ne idan ya zauna yana koyar da ita karatun addini, yana bata tarihin Annabi Sallallahu alaihi Wasallam, da sahabbansa wanda yake matuƙar ratsata da sanya mata nutsuwa da farinciki. Idan ta tafi birni, wurinsa ta san kullum sai ya bata tarihin Manzon Allah da wasu annabawan. Kuma ta huta da takurar baffa, a kan rashin fitowar manemanta, da an fara magana sai abu ya lalace, ya fara zancen ko iskokai ne suke hana maganar, ya saka ayi ta banka mata hayaƙi, dan an saka hayaƙi kuma sai ta hau suma, hakan ya sanya suke ƙara yadda da hakan. Bayan haka bijirewar jibo na zaman riga da zaɓar boko da barazanar da yake yi, ya ƙara sanya samarin garin nesanta kansu da Chubaɗo. "Chubaɗo, tunanin me ki ke yi ne?" Firgigita ta farka tana murmushi ta ce "Bakomai, daɗi nake ji, yau gani a bakin hanya, ina ta kallon motoci" sauran yan matasan suka din ga yi mata dariya, dan su suna zuwa, ita ce dai baffa baya barinta zuwa ko ina. Wani mutum suka hango yana tunkarosu, hannunsa riƙe da galan, gashi matashi a ƙalla zai shekara ashirin da bakwai, a ganinsu babba ne, amma sanye da ƙananan kaya, wanda hakan baƙo ne a wurin su. Yayi musu sallama suka amsa, ya ce "Yan mata dan Allah ina zan samu ruwa? Motata ta ɗauki zafi, a can baya na bar ta, kuma ina son zan yi salla, ruwan sha ne kawai a mota ta" Dukkaninsu kowa ya ce "Bai sani ba"' ban da chubaɗo, da tayi ƙuri da ido tana kallon kayansa, hamma yana saka irin kayan, kenan shi ma bayahude ne?. Ya ja ya tsaya cikin damuwa yana waige-waige, da alama kuma a gajiye yake. Kamar daga sama cikin siriryar muryarta ta ce "Na sani, amma ruwan  rafi ne, kuma a ɗan ciki ne" tayi maganar tana nuna masa hanya, yanayin hausar ya tabattar masa da cikakkiyar bafulatana ce, duk yan matan babu mai mayafi, suna sanye da kayan saƙi da ɗan kwali. Duk suka waiwaya suna kallon chubaɗo. Ya ce "Yauwwa yar albarka, nuna mini wurin" Cikin harshen fulatanci, suke gargaɗin ta a kan meyasa zata bi kaɗo, daga ganin sa yau. Ta ce "A tarihin Annabi da hamma yake bata, Annabi yana taimakon mutane, kuma babu kyau wulaƙanta mutane" ta wuce gaba ya fara bin ta a baya. Tayi gaba ba tare da ta ce masa uffan ba, tana ta kaɗa 'yar sandarta, tana cilla ƙafarta cikin nishaɗi. Ya ce "Ba a kusa ba, na gaji" ta tsaya ta waiwaya ta ce "To kawo abun ka zauna ka jirani, sai na ɗebo maka". Ya ce "A'a mu je" suka cigaba da tafiya, sun yi tafiya sosai, sannan suka ƙarasa rafin, ya durƙusa yayi alwala, ya ɗebi ruwa a galan ɗin da ya zo da shi. Yana satar kallonta, gaba ɗaya ba ta da wata damuwa, tana ta wasa da layar da take wuyanta ta sauko har kan ƙirjinta, hannu ɗaya kuma tana wasa da sandarta. Ya gama suka nufi komawa, ya ce "Ya sunanki ne?" "Mairamu" Ya ce "Masha Allah, sunana Bashir, ina yawan wucewa ta hanyar nan, ba taɓa zaton akwai mutane ba, ko daga wani wurin ku ke zuwa?" Ta ce "A'a rigarmu na can ciki" Ya ce "Masha Allah, mu je na sai nonon na sha, idan zan wuce na din ga tsayawa mu gaisa, ba zan manta da taimakon da ki ka yi mini ba" "Ba ni nake sayar da nonon ba, ni rako su kawai nayi, shanuna nake kiwo" "Au har kiwon shanu ki ke yi? Lallai ke jaruma ce" suka yi maganar lokacin da suka dawo in da ya tarar da su, ya sa nono mai yawa sosai, ya basu kuɗin. Ya ce "Mairamu, sai na sake dawowa, ni ɗan garin azaren jihar Bauchi ne, ta nan nake wucewa, sai mu din ga gaisawa na gode sosai Allah ya saka da alkhairi" ta amsa da amin. Suka koma gida, sai da aka gaya wa ramata mariƙiyar chubaɗo, ta bi wani kaɗo ta raka shi rafi, ramata tun daga ranar ta hanata bin su. Bashir ya daɗe yana wucewa, idan ya tambaye su ina mairamu, sai su ce masa an hanata zuwa. Ya ce idan sun je su gaishe ta. Sukan gaya mata, sai da ta ce musu to, amma bata ɗauki hakan da muhimmanci ba. Maitama ya sake zuwa rigarsu, sun fafata da baffa sosai, a kan ya bashi mairamu, amma ya hana shi, ya ce shi aure zai yi wa yarsa, ba za a kaita cikin kafurai ba. Ga surutu ya fara yawa a kan rashin aurar da chubaɗo duk da irin kyau da Allah ya bata. Maitama ya kawo mata ƙatuwar radio da carsets, na wa'azi da tarihin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam, ya koya mata yadda ake amfani da ita. Da daddare ƙawayenta da maƙwabtansu, zuwa suke su taru ta kunna musu, suyi ta saurara, idan wannan ya ƙare a saka wancan. Wani zuwa maitama ya zo da matarsa da ya aura, har da yara biyu da ta haifa, a wannan karon suka fara zuwa garin tare. Duk da haushin maitama da suke ji, sun karrama matarsa da yaransa sosai da sosai, sai dai a fili ta nuna ƙyamarta ga rigar, da nuna ita ba zata iya zama ba. Mairamu kamar ta haɗiye yaran nan, tayi ta ɗaukar ƙaramar tana goyawa, tamkar ta haɗiye su, da kyar suka yi sati ɗaya. Watanni shida suka shuɗe, mairamu ta sake bin ayari, zuwa bakin hanya wadda ta tasamma zama ƙaramar kasuwa. Ana ta hada-hada, kawai ta yanke jiki ta faɗi, numfashi ya sarƙeta, ya zamana ko motsi bata iya yi. Gaba ɗaya hankalinsu ya tashi, suka rasa yadda za su yi da ita, kamar an yi masa wahayi, sai ga motar Bashir, ya zo wucewa ya tsaya zai sayi nono ya wuce, ya hange su sun yi cincirindo a wuri ɗaya. Ya sauka ya fita, yana zuwa ya tarar da chubaɗo a baje a ƙasa ko motsi bata yi. Cikin tashin hankali yake tambayarsu, meyafaru da ita? Suka gaya masa faɗuwa tayi. Saroro suka yi, ganin ya taɓa ta, ba ta motsa ba, sai wani irin numfashi mai sauti daga ƙirji da take yi. "A garin nan kuna da Asibiti ne?" Suka ce "A'a, sai dai wurin mai magani" Bai yi sanya ba, ya ɗauki mairamu, ya sakata a motarsa, ya ce wasu daga cikin su su bishi, su tafi kaita Asibiti. Hama ce ta ce masa "A'a mufa rigarmu ba a zuwa asibiti" duk aka rasa mai bin sa, kawai ya shige motar ya ja ya tafi da ita. Cikin tashin hankali, suka kwashi kayansu, suka koma riga. A lokacin maitama yana gari, ai kuwa cikin kiɗimewa, aka yi ayari suka taho bakin hanya, amma babu Bashir babu alamarsa. Ramata kuwa tuni ta fara kuka tana salati, tana Allah ya rufa mata asiri ya sanya a ga mairamu, ba ita ta haifeta ba, amma akwai soyayya da shaƙuwa a tsakanin su. Sai dai suka dawo bakin hanya, amma babu Bashir babu chubaɗo, sosai Baffa ya din ga yi wa ramata faɗa, ta din ga kuka kuwa. Maitama ya ce su bari zai je asibitocin hanya ya duba, in dai da gaske kamar yadda sauran suka faɗa, asibiti ya ce zai kaita, to zai ganota. Baffa ya ce lallai sai dai su tafi tare, suka rankaya suka din ga duddubawa, ƙarshe a wani asibiti a nan jalingo suka gano mairamu. Maitama ya fara yi wa mutumin masifa, a kan dan meyasa zai ɗauke ta ya tafi da ita. Bashir ya ce "Ku yi haƙuri dan Allah, na san na ɗaga muku hankali, cikin yaran an rasa wanda zai biyo ni, na tarar da su da ita a gefen hanya, ba ta numfashi shiyasa kawai na ɗauke ta zuwa asibiti, in da muka fara zuwa suka turo mu nan" Baffa ya din ga faɗan shi baya zuwa asibiti, bai yadda da wannan abun ba, a ɗaukko masa 'yar sa ya tafi da ita. Maitama ya ce "A'a ba za ayi haka ba". Chubaɗo ta galabaita sosai da sosai, baffa ya cigaba da mitar, sai an bashi 'yar sa, za a kashe masa 'ya duk an ɗaura mata wasu kwanuka a fuskarta. Likitoci suka ce, ba zasu bayar da chubaɗo ba, ba ta warware ba, aka din ga kai ruwa rana da baffa, da kyar aka lallaɓa shi, ya ce yar sa ba zata kwana a wurin ba. Yamma sosai, Maitama yana son mayar da baffa gida, amma ba zai yiwu ya bar mairamu a asibiti ba, da mutumin da bai sani ba, ga lokacin babu waya. Ya lallaɓa baffa, ya kai shi tasha ya ce komai dare zai dawo masa da mairamu gida. Sai dai ya ga Bashir ba shi da niyyar tafiya, ya ce "Abokina mun gode da taimakon da kayi mana, zaka iya tafiya fa" Bashir ya ce "Ba zan iya tafiya na bar ta a halin nan ba, zan yi ta wasi-wasi ne. Dan ban manta alkhairin da tayi mini ba watanni baya" ya bashi labari. Nan hira ta ɓarke, yake bawa maitama labari, cewa shi coustom ne, ƙarshen wata yake komawa Bauchi hutu, yanzun ma gida zai tafi ya tsaya sayen nono, ya tarar da chubaɗo babu lafiya. Har yake bashi labarin, ainihi shi ɗan kasuwa ne, ya fi son harkar kasuwancin sa, amma aka turasasa masa wannan aikin, duk a takure yake. Shi ma maitama yake bashi labarin shi soja ne, nan da nan suka saba, suka din ga hira, kasancewar jikin da ɗan sauƙi. Yake gaya masa burinsa a kan mairamu tayi karatu, amma baffansu baya so, soyake lallai sai ya aurar da ita, ga shi bata da cikakkiyar lafiya. Suka kwana tare ta farfaɗo sosai aka bata magani, maitama ya ce ya samu dama, tafiya zai yi da mairamu can garin da yake aiki, a Benue state. Haka aka yi, asubar fari suka hau motar Bashir, ya je tasha in da ake hawa motar garinsu, ya bayar da saƙo a gaya wa Baffa, Bashir ya rage musu hanya, maitama yayi ta yi masa godiya sannan suka rabu. A hanya ya sake jaddadawa mairamu, zai tafi da ita gidansa da yake zaune, taji daɗin hakan, sai dai ta wani fannin ta ji kewar gida, yadda aka rabota da garin babu ko sallama. A cikin barrack gidan sa yake, matarsa kawai sai ganinsa tayi da mairamu, dan hatta kayan sakawa a hanya ya saya mata. Bayan ya huta take tambayarsa, lafiya ta ganshi da ita, ya sanar mata ta dawo nan da zama, nan ta ce bata yarda ba, shi kuma ya ce to ta koma gidansu, shi zai rayu da ƙanwarsa. Ta ɗauki gaba da fushi da shi, shi kuwa ko a jikinsa, chubaɗo bagidajiya ce a birni, ba ta iya komai ba, ta din ga ganin abubuwa kamar ba a duniya ake ba, maitama da kansa ya din ga koya mata abubuwa. Baffa ya rikice kamar yayi hauka, bayan samun saƙon maitama, na ya tafi da mairamu. Mairamu daga ita sai maitama, sai yaran gidan take mu'amala da su, hatta amfani da kayan wanka komai shi ya koya mata. Satinta uku a garin, babu alamar musulmai a in da suke, duk sati maitama yake kaita ganin likita, saboda matsalar ta. kwatsam sai ga Bashir. Abun ya basu mamaki nesa ba kusa ba, wai duba mairamu ya zo. Nisan tafiyar kawai maitama ya din ga hangowa, suka karɓe shi, suka karrama shi sosai da sosai, ya din ga murnar ganin mairamu ta samu lafiya. Sai da ya kwana a garin sannan ya koma. Sai dai bayan wata guda ya sake dawowa, a lokacin maitama ya saka mairamu a makarantar boko, karatun addini kuma, yana koya mata a gida. Duk wani aikin gida, mairamu tana yi wa matar hammanta, amma sam bata gani, kawai ta tsaneta. A wannan karon, maitama ya rutsa Bashir, a kan ya gaya masa dalilin zuwan da yake yi, bai yi ƙwauron baki ba, ya sanar masa son mairamu yake yi. "Kana mutumin birni, tayaya zaka auri bafulatanar daji, yarinya ƙarama?" Ya ce masa shi babu komai zai iya yana son ta a haka, sai dai da magana ta yi magana, ya sanar masa yana da mata biyu. Maitama ya ce yayi haƙuri, ba zai iya aura masa mairamu ba, duk da matashi ne, ko talatin bai yi ba, amma yana da abin hannunsa, ya ce yarinya ce yar ƙauye mara wayo wahala kawai zata sha. Sai dai mairamu, bai gaya mata yana son ta ba, amma maitama ya lura da yadda take murna idan ya zo. Sai dai hakan bai hana shi, sake niƙo gari ya zo Benue ba, saboda mairamu. Maitama ya sake jadda masa, ba zai bashi mairamu ba, ya ce shi in dai zai zo ya ganta shikenan, haka ya cigaba da sintiri. Wani zuwa da yayi, ya bata wasiƙa lokacin da ya zo, ta zauna ta karanta ta kasa, saboda manyan turanci ne, ta kai wa hammanta ta ce ya karanta ya fassara mata, ita ba ta san me aka rubuta ba. "Kalaman soyayya ne" ya bata amsa. Sai tayi shiru tana mamakin wace irin soyayya kuma?. Tana kewar baffa da kuma dada, amma tana jin tsoron gaya wa hamma yayi fushi. Sai da ta shafe watanni biyar, sannan maitama ya je riga, aikuwa ya sha takaici, dan ƙiris ya rage baffa yayi masa baki, ya ce ya dawo masa da 'ya ya aurar da ita, kar ta lalace. Maitama ya ga idan ya dawo da ita, ba zata cigaba da samun kulawa ba, saboda yadda suka jahilci zamani da cigaban da ya zo da shi. Ya ce "To yanzu akwai mijin da zaka aura mata ɗin?" "A'a amma zan samo mata" "Ni ina da wanda zan aura mata, idan ka yarda ya zo ya nemi aurenta" ya ce bai yarda ba. Aikuwa maitama ya ce ba zai dawo da ita ba, in dai a garin nan za ayi mata aure, idan ya tafi ba zai dawo ba har abada, kuma ba zai sake ganin mairamu ba. Ba shiri ya amince, ya turo masa mijin da ya samo matan. Yayi tattaki har azare, yayi bincike sosai a kan bashir, ya tarar da familynsu mutanen kirki ne, shi kansa nagartaccen mutum ne, har wurin da yake aiki, sai da ya je duk ya kammala binciken sa, sannan ya koma ya tuntuɓi mairamu idan tana son Bashir, tayi shiru ta sunkuyar da kai, hakan ya sanya ya gane in data dosa. Ya nemo Bashir da kansa, ya gaya masa halin da ake ciki, amma ya ce zai bashi auren mairamu, idan ya amince da zai riƙeta amana, ya kula da lafiyarta da iliminta, a duniya ba shi da kowa sai Allah sai mahaifinsa da mairamu, itakaɗai ce yar uwassa. Bashir ya ce ya amince kuma yayi masa alƙawarin haka. Ya tura shi wurin baffa, nan ma sai da aka yi wani darun, ya ce ba zai bayar ba, da shi aka haɗa baki, jibo ya gudu da maitamu, maitama ya tsaya, tsayin daka, Baffa ya bayar da auren mairamu ga Bashir. Ya dawo da ita aka yi biki da ɗaurin aure, aka kai mairamu gidan Bashir da yake jihar Bauchi. Matan Bashir sai da suka kusa yi masa bore, jin zai auro musu, yarinya ƙarama bafulatanar daji, amma ya ce babu gudu babu ja da baya. Ba wata shaƙuwa suka yi da Bashir ba, dan haka wata irin matsananciyar kukyarsa ta din ga ji. Washegari kaita, ya tara matansa a falonsa, ya gabatar musu da mairamu. Sai dai sun sha jinin jikinsu, ganinta jawur kamar ƙosai, dai-dai gwargwado kyakykyawa ce ta gaske, kuma yarinya sharaf. Shi kansa ba wani babba bane ba, amma ya ajiye mata uku rigis, yayi musu nasiha sosai, ya ja amaryar sa ɗaki. Ita ma yayi ta yi mata nasiha, yana yi yana gaya mata kalaman soyayya, ta ja gefe ta duƙunƙune a mayafi, saboda kunya. Ko riƙe hannunta taƙi yadda ya yi, ya nuna mata yaransa, a lokacin yaransa huɗu, biyu maza biyu mata. A da kan ya auro, mairamu faɗa da kishi a tsakanin su, kamar sun cinye junansu, amma tun da yayi aure suka haɗe masa kai. Mairamu na da tsananin biyayya, da safe sai ta durƙusa ƙasa, zata gaishe shi. Suna da mai aiki, idan aka gama abinci, za ta je ta ɗaukko masa, amma ba zata taɓa cin abinci a gabansa ba, saboda kunya. Ana gobe zai bar ɗakinta, ya cika kwana bakwai, sannan wani abu ya shiga tsakaninsu. Kasancewar kowa ɗakinta ciki da ƙaton falo ne, banɗakuna biyu ne a tsakar gida, sai kuma banɗakin da yake cikin ɗakinsa falle ɗaya. Amma a ɗakinta ya kwana, cikin dare yana ƙoƙarin taimaka mata, ta kintsa, uwar gidan ta dalle su da fitila a tsakar gida, ta din ga zuba habaici da rashin mutunci. Da sassafe ta zo ƙofar ɗakin ta ce ya fito, tun da yau girkinta ne. Sai wajen la'asar, ya samu sukunin sake shiga ɗakin chubaɗo, ya tarar da ita a kwance, abincin ma da aka kawo mata ba ta ci ba. "Fulanina, sannu ya jikin?" Ta ƙunshe fuska ta ƙi magana. "Ba ki ci abinci ba, me zan sayo miki ki ci?" Ta girgiza masa kai alamar babu. Ya kwantar da murya ya ce "Tashi na baki abincin a baki, ai za ki ci ko fulanina" Fafur taƙi sai ma ta saka masa kuka wai gida, ya mayar da ita gida. ya tashi ya fita ya sayo mata tsire fal, da fanta ya kawo mata. Ya din ga rarrashinta, da ƙyar ta daina kukan, ai ba ta saurari nama ba, ta din ga ɗaɗɗakar fanta. Yayi murmushi ya ce "Ka ga bafulatanar Bashir, da ga yanzu na gano lagonki, fanta ce maganinki" sai kuma ta sunkuyar da kai tana murmushi. Sai da ya shafe wata guda a Bauchi, ya kaita can garinsu azare, da yake shi ba a can yake zaune ba, a can ya samu ya ɗan sake da ita sosai, dan sai da suka kwana uku, sosai danginsa da yan uwansa suka karramata. Mamaki take yi yadda yake salihi, a gaban mutane, ake yi masa kallon mutumin kirki, yake sunkuyar da kai, amma ida suka keɓe yayi ta yi mata fitsara da rashin kunya. Wata irin soyayya yake yi mata, wadda bai iya nuna mata a waje ba, dan da gaske yake jin sonta a cikin ransa, chubaɗo akwai haƙuri da biyayya, ya samu har ta ɗan fara sakewa da shi, yayi kamar ya ce zai tafi da ita in da yake aiki, dan dab da za ayi bikin su, aka mayar da shi Naija state. Da ya fara yi mata wani abu dan soyayya da kyautatawa, sai ta ce ya bari, saboda tana son ta shiga aljanna. Ya dubeta ya ce "Waye ya ce idan na yi miki tausa, ko dafa miki ruwan wanka, ba zaki shiga aljanna ba? Jin dadin biyayyar da ki ke yi mini, ya sanya nake yi miki abin da zaki ji daɗi kema" "To zan shiga aljanna?" "In sha Allah, hannuna a naki zamu shiga" Ta rausayar da kai ta ce "Wataƙila babar saifu ta hanaka, ta ce na ta hannun zaka riƙe ita da amarya, ku tafi ku barni" tayi maganar cikin kishi da yarinta. Yayi dariya ya ce "Kowaccenku, zan riƙe hannunta mu shiga tare in sha Allah" Mairamu bata aikin komai, gidan ma kusan ba wanda yake wani aiki a gidan, saboda suna da masu yi musu aiki. Da fari tana so ta ɗan sake da matan gidan, amma suka nuna mata bata isa ba, hatta masu aikin ma wani gani-gani suke yi mata. Sai dai saifullahi ne mutuminta, shi ne ya kan shigo ɗakinta, har su ci abinci tare da shi. Tun da Bashir ya koma aiki, suka mayar da mairamu tamkar baiwarsu, suka din ga sakata ayyuka na wahala, suka dakatar da mai aikinsu, ita ce wanke-wanke, shara raino wankin yara da kuma girki. Gashi har a lokacin da ƙauyanci da ƙuruciya a kanta. Maƙwabta suka din ga ziga su, wai ƴar aiki kawai aka kawo musu, ban da haka ina wannan bagidajiyar zata iya kula da miji. Ranar da zai dawo, duk sun sha ado da kwalliya, mairamu kuwa futu-futu dan wuni tayi tana aiki. Duk zumuɗin ya zo ya ganta, bai ji daɗin ganinta a haka ba, da ya shiga ɗakinta sai da ya ce mata ƙazama. Haƙuri kawai ta bashi ta yi shiru. Ranar da ya dawo ɗakinta, ta yi kwalliya, hakan yayi masa daɗi sosai da sosai, babban abin da ya basu mamaki, bai wuce jiyo dariyar Bashir da mairamu ba, suna yi mata kallon sokuwa, amma ta saka miji a ɗaki suna ɓaɓɓaka dariya. Tambayarta yake yi "Da a baki fanta, da nagge wanne ki ka fi so?" Ta ce "Kai Nagge mana" Ya ciro check, ya rubuta Naira dubu ashirin irin ta da a jiki, ya ce "Nan dubu ashirin ne, da na baki wannan, da na baki nagge wanne ki ka fi so?" Tayi dariya ta ce "Aradu na fi son nagge" suka tuntsure da dariya ya ce "Baki da wayo, wannan kuɗin sai ya sai miki nagge biyar" "Wannan ɗin, takadda ce fa kawai gaskiya na fi son nagge" Bashir ya ce "To da ni da nagge wanne ki ka zaɓa?" Ta waro ido. Ya ce "Sai kin zaɓa fa" Ta faki idonsa ta ce "Nagge"ya riƙeta yana yi mata cakulkuli ya ce "Me ki ka ce?" "Kai na zaɓa" tayi maganar tana dariya. Mairamu ba ta taɓa kai ƙarar wani wurinsa ba, su kuwa ba sa rasa Sharrin da zasu yi mata, wani ya yadda wani ya rabu da su. Ba ta taɓa cewa ya sai mata wani abu ba, duk da yana jaddada mata, duk abin da take so, ta tambaye shi. Maitama ya zo gidanta bayan auren, sai dai yayi farinciki da yadda ya tarar da mairamu, babu yunwa babu ƙishirwa, akwai kulawa sosai da sosai. Duk da kashedin da Bashir yayi musu a kan mairamu ba ta da cikakkiyar lafiya, bai hana idan baya nan su azabtar da ita ba su tura ta gaban hayaƙi ba. A gidan Bashir ta fara al'ada, shi ma sai da matan suka yi ta ƙanan maganganu, dan sun zata ciki ne da ita. Ana haka Allah ya yi wa baffa rasuwa, babu wanda ya sani, dan sai da yayi watanni uku, sannan maitama ya sani, ya saka aka gaya wa Bashir. Chubaɗo ta sha kuka, kamar babu gobe, ta shiga matsananciyar damuwa da tashin hankali. A haka ta shafe shekara guda cif, dada ta zo mata, ta ji daɗin hakan, sai dai sai da suka kuma yin kukan rashin baffa. Dada ta din ga rarrashin mairamu, dan ta fuskanci yanayin zamanta da abokan zamanta babu daɗi, amma gidan akwai kulawa komai na buƙata akwai. Sai da ta shekara biyu, ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba, ko a jikinsa, ita dai tana ta addu'a, Allah ya sa ita ma ta haihu, dan yar da aka haifa hafsa kamar ta ce a bar mata, duk da idan ta  ɗauka ayi ta yi mata habaici. Aka kuma canzawa Bashir wurin aiki, ya samu ƙarin matsayi, ga aiki ga kaswuanci, ya sai wuri a kano, ya fara gini, saboda yana ƙaunar garin kano, yana son idan ya gama, su koma can, ya nemi transfer ya dawo arewa gaba ɗaya, dan a kano ya auri matarsa ta biyu, kuma garin ya burge shi. Watarana da safe, ana shirin karyawa, jaririya hafsa ta fara rarrafe, mairamu ta ce "Ki kula kar hafsa ta ɓaro kunu a jikinta" aikuwa tana rufe baki, hafsa ta sheƙo kunu a jikinta, ta ƙone, tun a ranar suka laƙaya mata maita. Haka kurum ta fara rashin lafiya, abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, ga Bashir ba ya gari, aka rasa mai kaita Asibiti, abu har da suma, ciwonta kuma ya tashi, sai masu aiki ne suka kaita Asibiti, a tsukin lokacin Bashir ya dawo, ya sha baƙin ciki da ɓacin ran abin da suka aikata. Duk ta rame ta yi duhu, ya mayar da ita Asibiti da kansa, aka tabattar masa da tana da juna biyu. Ya din ga murna kamar ba a taɓa yi masa haihuwa ba, sai dai yayi shiru da bakinsa, da ya tashi komawa aiki, ya ce da ita zai tafi. Suka yi surutansu da masifarsu, suka gama. In da aka mayar da shi aiki, can wani gari ne a kudancin Najeriya, a lokacin rabonta da hammanta, kusan shekara duk ta damu tana son zuwa ganin gida, ya ce ta bari idan ta kusa haihuwa, zai mayar da ita gida ta haihu ta yi arba'in. Lokacin maitama shi ma babu zama, daga wannan gari zuwa wancan gari, har ƙasashen da ake yaƙe-yaƙe a Afrika ake tura su aiki, dan haka bai samu sukunin sake zuwa wurin mairamu ba, sai dai kullum tana zuciyarsa. Tana yawan yi wa Bashir zancen makaranta, ya ce zai mayar da ita, yana sane, dama target ɗin sa, ta haihu ko ɗa ɗaya ne, sai ya sakata a makarantar. Ashe matansa sun ƙwafe tafiyar da ya yi da ita a ransu, sun ƙullace su, dama a hakan a rashin wayon nata, da azabar da suke yi mata, gani suke yi ta mallake shi abin da take so kawai yake yi. A can garin kuwa, yana bata kulawa iya yin sa, amma laulayi ya sakata a gaba, ciwonta kuma kusan kullum cikin tashi yake, shi yake yi mata komai yake kula da ita, cike da ƙauna da tausayawa, bai taɓa gajiyawa da ita ba, sosai yake tausayinta, ba ta da wasu dangi, da za ace su zo su kula da ita, ko ya kaita tayi rainon cikin a can, dan har ga Allah ba zai iya kaita rigar nan tayi rainon cikin a can ba. Idan ya samu lokaci, yana zuwa can gidan, ya yi kwanaki ya dawo, cike da addu'a da fatan Allah ya sauketa lafiya. Cikinta na da wata takwas, ya je gida, tun da ya je, gaba ɗaya tamkar an shafe masa duk wani tunani da ya shafi mairamu, yazo da kwanaki biyu, aka turo masa da takardar transfer, an mayar da shi aiki jigawa. Bai ko sake komawa garin da ya baro marainiyar Allah ba, ya je yayi reporting a wurin aikinsa na Jigawa. "Abba, ina ga canza hanya zamu yi, akwai go slow sosai a nan, maganar Nasir ta dawo da Abba daga tunanin da yake yi. Ayshercool 08081012143 85 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Major yayi wata irin nannauyar ajiyar zuciya, ba tare da ya ce komai ba. Nasir ya ce "Abba" "Nasir, ko ma ta ina ne ka bi, fatana kawai na cimmusu, shi kansa yaron na ji dalilin sa na shiga sha'anin iyalina ba tare da izinina ba". Nasir ya ce "Ina ga hakan baya rasa nasaba, da ta jikin hoton da na kawo maka" Abba yayi shiru bai sake cewa komai ba. Viper kuwa muryar Abbu ce ta cigaba da amsa kuwwa a cikin kunnuwansa, ya din ga jin muryarsa har cikin ƙirjinsa. Gefensa Nabila ta na ta kuka, ba yadda ya iya, ya ji zuciyarsa babu daɗi sam. Ya matsa murya ƙasa-ƙasa ya ce "Ki daina yi mini wannan kukan, na gaya miki ba na so ko?" Shiru tayi masa ta cigaba. "Babu buƙatar mu je in da zamu je, kina kuka a haka, idan kuma mu koma ne shikenan" Cikin kukan ta ce "Ni ku tsaya ku sauke ni, koma ina ne ba zan je ba" Ya ce "Saboda me?" "Yanzu ku ka gama ci mini mutunci da kai da abokanka, bani da kamun kai, ina yawo a cikin maza, kai kuma dan na haɗaka da mahaifinka, ya zama tashin hankali, har ka manta har da fushin iyaye ya jefa ka a musibar da ka ke ciki, daga ƙoƙarin sasanta ku, wataƙila komai ya zo mana ma da sauƙi a dalilin hakan, amma kalli yadda ku ke cin fuskata, wallahi ƙaddara ce ta kawo ni in da ku ke, har gaban iyayena na bari nayi karatu, ban lalace ba, kuma ban saki jiki da maza ba, duk aikin ƙaddara ne, da ƙoƙarin ceto rai, amma bakomai na gode" Sai kuma jikin liti yayi sanyi, Walid kansa bai ji daɗin abin da suka yi wa Nabilan ba. Walid ya ce "Yi haƙuri Nabila, dan Allah ki ke yi ba dan halin su ba, kuma Allahn yana gani, shi ne zai biya ki, idan ki ka gama shari'ar nan, duk ki watsar da su ki yi ta kanki, kar wanda ki ka sake nema. Wallahi ni ina gani, kuma ina yabawa abin da ki ka yi" Liti ya ce "Walid ba a haka, wannan ai ziga ce, ke yi haƙuri haushi ki ka bani ne" Zazzage jakarta ta fara yi, saboda numfashinta baya sauka cikin ƙirjinta sosai, saboda kukan da ta yi. Viper ya taimaka mata, ya ɗaukko mata inhaler ya saka a bakinta, sau biyu ya fesa mata, ta saka hannu ta karɓa ta mayar ta saka a cikin jakarta, tana share hawaye. Message ya rubuta mata a wayarsa, ya tura ta ta, ya miƙa mata ta karanta, ɗagowa ta yi ta kalle shi, suka haɗa ido, ta galla masa harara ta gyara zamanta, tana kallon taga. *** Asibiti kuwa sai da aka je da 'yan sanda, sannan suka karɓi rahila, shi kuma Abba aka je aka kamo shi. Tuni labari ya karaɗe gari, yaro ya yi wa uwassa duka, a kan tayi masa faɗan daina ta'amalli da kayan maye. Hannunta na hagu ta samu karaya, har guda biyu, ga gefen wuyanta da ya kumbura yayi suntum saboda duka. Abbu ya ce "Daga hannun yan sanda sai dai su san yadda za su yi da shi, dan ba zai sake zamar masa a gida ba, ya koma hannun ubansa. Abun takaici sai dangin rahila suka fara ƙananan maganganu wai da ɗansa ne, ba zai ce zai kore shi ba, tun da abin ƙaddara ne, bai wuce kan ɗan kowa ba. Abbu ya ce "Ai ba ɗan nawa bane, nawa ɗan ma da ya ƙi ji bai ƙi gani ba, dan haka ba zai yi mini kisan kai a gida ba, tun da ya iya dukan uwarsa wataran ai ni zai daka" "Yo Allah na tuba kisan kan, ai kai ba ka yi wa wani gorinsa ba, tun da dai kai ma naka ɗan yayi, kuma in sha Allah, Allah ba zai nuna mana wani yayi kisan kai a zuriyar mu ba" Abbu ya ji zafin maganar da ƙanwar uwar rahila ta gaya masa, amma ya haɗiye yayi shiru, bai ce uffan ba ya fice ya bar su. *** Ramma abin duniya ya isheta, wata irin kewar Abdul take yi kamar babu gobe, Abdul ɗan gayu ne kuma ɗan hutu, tun da ta ji an ce an kama shi, sai ta ji gabanta na tsananta faɗuwa, da zata yi masa adalci roƙonta da ya din ga yi, ta yafe masa yakamata ta yafe masa, da fari ta zata idan aka kama shi, aka hukunta shi zata huce, amma sai ta ji ba haka ba, tausayin sa ma take ji. Gashi mahaifiyarta, ta saka ta a gaba, ko saurararta ma ba ta yi yanzu, ta kuma dage a kan lallai idan tana son su zauna lafiya, to sai an zubar da cikin nan, da ba zata taɓa yarda ta haɗa zuriya da marasa mutuncin mutane irin su Abdul ba. Gaba ɗaya dauɗa ce take bin zuriyarsa babu na Allah cikin su, mussaman zaluncin da aka yi wa ɗan ta Nura, wanda hakan yake ƙara tunzurata ta ji tamkar ta yi wa ramma shegen duk ko zata huce. *** A nesa kaɗan da ƙofar gidan suka yi parking, Viper ya ce "Bari na je tukuna na dawo, ku jira ni ina zuwa" Walid ya ce "To shikenan, babu matsala" "'yar sugar am talking fa" yayi maganar yana kallon ta. Haɗe rai ta yi ta share shi, tana ta tura baki, tana son tayi masa tsiwa, amma ta kasa sai harararsa da take ta gefen ido. A zuciyarsa ya ce "Allah ya bamu ikon cin wannan jarrabawa" ya sauka daga motar, ya nufi gate ɗin gidan, yana yaba cigaban da suka samu, dan wannan gidan na su ya fi na cikin gari kyau da suka baro, nesa ba kusa ba. Ya tsaya a bakin gate ya fara bubbugawa. Wani yaro ne ya buɗe, yana cewa waye, Viper ya ce "Ka je ka ce ana sallama" yaron ya ce "To" ya koma cikin gidan, mintuna kaɗan Tijjani ya fito, kawai suka yi arba da Viper, ya kalle shi, shi ma ya kalle shi. "Me ka zo yi mana gida kuma?" "Wurin Baba na zo" "Zai fi kyau ka kira shi da sunansa kawai, ba sai ka yi masa kara ba, bayan ka kashe masa 'ya" Kai tsaye maganar ta soki, tsokar da ke tsakanin ƙirjin Viper wato zuciya, amma ya dake ya ce "Ina son ganin Baba, ka yi mini iso wurinsa" "Ba zan yi ba, baka da abin da zaka gaya masa.... "Shhh Viper ya faɗa, a lokacin da ya ɗaga wa Tijjani, rigarsa. Ya hangi ƙyallin iraƙi a ƙugun Viper "Haryanzu ina nan a yadda ka sanni, in saka maka ƙarfe, in tsallake ka, na shige gidan nan, ba zai zama sabon abu ba, a abin da na saba aikatawa ba, ka shiga ka yi mini iso da mai gidan" gummm tijjani ya rufe bakinsa. Baba kuwa ya san da zai yi baƙo, sai dai bai san wanene ba, dan an kira an tambaye shi ne kawai yaushe za a same shi a gida, ya bayar da wannan lokacin. Yana zaune a falonsa, yana karanta jarida, Tijjani ya shigo yana zazzare ido. Mama ta ce "Lafiya kai da waye a wajen ne?" Wata irin zazzafar ajiyar zuciya ya sauke, ya ce "Mijin jauhar ne a waje, wai yake son ganin Baba" gaba suka yi sak suna bin sa da kallo, a gigice Abba ya tashi ya ce "Wace jauhar ɗin? Waliyiyya dai? Kana nufin Al'amin?" Ya jero masa dukkanin tambayoyin lokaci guda. Zakiyya ta ce "Ya zo yayi mana me, ko kuma ya ce me? Shi har yana da kunyar sake tunkaro mana gida, alhalin ya kashe mana 'ya? Kenan da gasken dai sakinsa aka yi, yake yawonsa a gari yadda yake so?" Hanyar fita Baba ya tunkara, Tijjani ya riƙe shi, ya ce "Dan girman Allah baba kar ka fita, yanzun ma da makami a jikinsa, kar yayi maka illa, ba fa mun san meya kawo shi ba. Can waje kuwa, Saifu ne ya dawo, ya ajiye motarsa ya fito ya nufo shiga gida, kawai ya ga Al'amin a tsaye. Kamar mai mafarki, haka ya ƙarasa gaban gidan, yana kallon Al'amin. Ya ce "Kamar mai zamani mijin jauhar?" Viper ya kalle shi, bai ce komai ba. "Me ka zo yi mana gida, saboda rashin kunya da rashin ta ido, sai yanzu bayan shekaru shida, ka zo ka kalli fuskokinmu, kaga wani hali ka sanya mu a ciki, bayan sakayyar da ka yi mana, aka ɗauki 'ya mafi haƙuri da tarbiyya a gidanmu a ka baka, duk tausayinta da soyayyarta gare ka bai hana kashe ta ba, ka zo ka yi mana gadarar iyayen gidanka sun sanya an sake ka ne kamar yadda ka saba?" Yayi maganar idanunsa na cika da hawaye. "Har duniya ta naɗe, ka bar mana mummunan tabo a zukatanmu, tabon da ba zamu taɓa yafe maka ba, babu yadda ban yi da ita a kashe auren nan ba, amma taƙi ta dage, ita na rabu da ita tana son aurenta, ta san zaka shiryi, zaka daina duk abin da ka ke yi, amma kalli irin ƙarshen da tayi duk a dalilin rashin imaninka, wallahi ba zamu yafe ba" Viper ya ƙurasa masa ido, ya rasa abin da zai ce masa, duk da a baya ba wani shiri suke yi ba, amma yana ɗagawa saifu ƙafa, saboda yadda jauhar take yin sa, take yawan zancensa da shi da hafsa, mussaman ma shi. Tabbas ya cancanci ya shanye duk wani abu da za a gaya masa yau, komai ya samu shamuwa watan bakwai ne ya janyo mata. Cike da ƙosawa Nabila ta ce "Ni fa gaskiya na gaji, wai me yake faruwa ne?" Walid ya ce "Ki ɗan ƙara haƙuri kaɗan, za ki ga koma menene" Babu yadda Tijjani bai yi ba, amma fafur baba yaƙi tsayawa, yayi waje a sukwane. Viper yana ido huɗu da mahaifin jauhar, kawai sai ya karaya, gabansa yayi mummunan faɗuwa, bugun zuciyarsa ya ƙaru, jikinsa yayi sanyi ƙalau, ji yake yi kamar ƙafafuwansa na neman gazawa da ɗaukarsa, bai san ma da wane idon zai kalli baba ba, bai san me zai ce masa ba, rabonsa da shi tun kan mutuwar jauhar, da ya kawo musu ziyara da daddare, har Viper ya kusa abun kunya, bai san baba yana gidan ba, ya shigo yana mitar "To uwar son kuɗi, yau ba oyoyon babu ɗan karairayar, Allah ya sa ba neman kuɗin ki ka ƙule a ɗaki ki na yi ba" tana gaban baba, amma kamar ta nutse, sai da ya shiga falon ya ga baba, kamar ya juya ya koma saboda nauyinsa da ya ji. Baba yayi murmushi ya ce "Ka sanya a ranka ban ji komai ba, ni babu abin da na ji" Da kyar ya iya shiga suka gaisa, sun jima suna hira, har baban ya ba wa jauhar ruwan tofi da ya karɓo mata, wai saboda haihuwa. Ya na ta murna da ɗokin, zai ɗauki jika ta wurin jauhar. Da Baba zai tafi, Viper ya raka shi, ya cigaba da yi masa nasihar ya nutsu, ya zama mutumin kirki, saboda yana daf da zama uba, yayi ƙoƙarin zama uba nagari ga abin da za a haifa masa. Viper yayi masa alƙawarin hakan, tare da tabattar masa, duk wani abu da zai gusar masa da hankali, ko yayi ɓarna, yana ta iya ƙoƙarin sa a kan dainawa, kuma cikin ikon Allah ya rage kaso mafi yawa. Baba ya nuna masa jin daɗin sa a kan haka, tare da yi masa addu'a. Ba ayi sati da zuwa gidan ba, tsautsayin nan ya faru, kuma ko a kotu, bai ga Baba ya je ba. Viper cikin mamaki, ya ga Baba ya rungume shi, ya ce "Sannu Al'amin, sannu da zuwa" ya riƙo hannunsa, ya buɗe gate ɗin gidan, yana jan hannun Al'amin. Saroro tijjani da saifu suka bi baba da kallo, duk tsawon lokacin da ya shafe, yana gaya musu bai yadda Al'amin zai kashe jauhar ba, ba su yadda da gaske yake ba, dan ya ce musu babu wata gamshashshiyar hujja a kan hakan. Suka ankarar da shi cewa, yana ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, dan haka ba abin mamakin bane ba, amma ya ce shi dai har zuciyarsa bai amince da hakan ba. Har tsakiyar falonsa ya shiga da shi, cikin murna da farincikin ganin sa, ya ce "Zakiyya, ku kawo masa ruwa, sannu Aminullahi amintaccen Allah, dama zan sake ganin ka bayan na rasa Waliyiyya? Sannu Aminu" kawai Viper ya durƙusa a kan gwiwoyinsa, ya riƙe hannayen Baba, ya ɗaga ido ya kalle shi, ya ce "Wallahi baba ban kashe jauhar ba, ban kashe waliyiyya ba, me tayi mini me zai sanya na kasheta? Idan da wanda zai tafka asarar mutuwarta to ni ne, ni ne nan baba, zan yadda idan aka ce nine sila, amma da hannuna ban kasheta ba baba, ba ni na kashe maka jauhar ba, na san duniya ba kowa zai yadda da hakan ba, amma na san ko yaya, kai zaka yarda da ni Baba, wallahi ban kasheta ba, nayi burin kashe kaina nima, ko dan kaucewa sake haɗuwa da kai, ban san me zan ce maka ba, ban san da wasu kalmomi zan yi amfani ba, kawai dai ban kasheta ba" Cikin rauni, da dattaku, Baba ya rungume Viper a kan kafaɗarsa, yana dukan bayansa cikin sigar rarrashi, ya ce "Ko kowa bai yadda ba, wallahi ni shaida ne Aminu, ni na san me na gani, na san me na ji daga bakinta a kanka, kar ka damu, na san me ka ke ji, na taɓa tsintar kaina a yanayi mai kama da naka, ina fatan Allah ya yi wa jauhar rahama, Allah ya sa halinta na gari ya bi ta" "Nayi asarar mace Baba, ta bar ni da raunin da ba zai taɓa gogewa a zuciyata ba, ba zan fasa zargin kaina da ni ne silar mutuwar jauhar ba, taurin kai da jinkirta barin aikata laifi, shi ya janyo mini haka, ina kewar matata" tamkar ƙaramin yaro, haka ya kwantar da kansa a kafaɗar Baba yana kuka, kukan da ya daɗe yana fatan Abbunsa ne ya fuskance shi ya bashi wannan damar. Baba ma kukan yake yi, ya ce "Haka Allah ya tsara, ka yi haƙuri, mu duka na haka ne, zaman jiranta muke yi. Bayan an kama ka, mijin yayarta hafsa da ya so ya aureta, shi ya zo ya same ni, ya ce mini in ci gaba da addu'a, Allah ya bayyana gaskiya, amma ba kai ka kashe jauhar ba, abin ne akwai sarƙaƙiya, duk da ni dama tun farko ban yadda zaka kashe mini 'ya ba. To kuma daga baya ita ma hafsan zaman yaƙi daɗi, suka rabu". Viper ya ɗago ya kalli Baba cikin mamaki, ya ce "Shi ne ya zo ya ce maka bani na kashe jauhar ba?" Baba ya jinjina masa kai, ya ce "Eh, shi ya gaya mini haka" Viper ya sauke numfashi ya share gumin da ya haɗa da hawaye, da handkerchief ɗin sa. Gaba ɗaya cirko-cirko mutanen gidan suka yi, suna mamakin baba, yadda ya sake da Al'amin, wataƙila ma ƙarya kawai yake ta zuba masa, dan kawai a tausaya masa. Viper ya ce "Na zo da wata tambaya da nake buƙatar amsarta baba" Baba ya ce "wace tambayar ce?" "Baba jauhar mutum nawa ce?" Cikin mamaki baba ya ce "Kamar yaya?" "Tana da wata 'yar uwa ne, da suke ciki ɗaya?" "A'a itakaɗai ce" Ya jinjina kai ya ce "Akwai lauyata, da muka zo tare, zaku tattauna da ita, wadda ita ce tambayata da nake son ka amsa mini" ya tashi tsaye, ya nufi hanyar fita. *** "Kankarofi, zuwa yanzu ina fatan hankalinka ya kwanta baka da wata damuwa ko?" Ya kalli indabo ya ce "Ba ni da ita Indabo, kawo ƙarshenka, babbar nasara ce, da rage mugun iri a ƙasa ko ma na ce duniya baki ɗaya" "A'a, bari murna karenka ya kama zaki, da saura tukuna baka kawo ƙarshena ba, kuma kawo ƙarshena tamkar kashe maciji ne, baka sare kansa ba" Kankarofi ya ce "Ko ban sare kansa ba, ya tashi, na rage masa karsashi da ƙarfin mugunta da zalunci. Kuma in sha Allah wannan kujerar da ka cimmata, ta hanyar zubar da jinin mutane bisa zalunci, da amfani da rayuwar talaka ka cimmata, ka wofantar da su ka tagayyara rayuwar su, sai ka barota, sai ka kuma fuskanci hukunci. Yanzu haka ana shirin tsayar da kadarorinka, a kai gaban shari'a bisa laifin sata wato cin amanar ƙasa, bayan babban tattalin arzikinka da aka kama, na miyagun ƙwayoyi a Italiya. Ka san Waye yayi maka aikin kama ɗanka da kama maka dukiya? Viper! Abin ya baka mamaki ko? Wani banbarakwai, da yake ce maka ya saka an kama ɗan sa ka daɗe kana mamaki, da ganin ƙarya yake yi. Dodo babban sarki ya fi ka lissafi, da shu'umanci indabo, sirrinka da ya sani, ya san zaka kashe shi, ba za ku bar shi da rai ba, da shi da tawagarsa, shiyasa ya ƙara jan Viper, ya sanar masa da duk wani abu da yakamata ya sanar masa. Duk tsawon lokacin da Viper ya shafe tare da kai... Yayi shiru yana kallon Indabo. "Spy ne, hatta yadda ka ke samun return da kai da tawagarka, a kan tashe-tashen hankulan da ake yi a ƙasar nan, yadda ku ke safarar makamai ta ɓarauniyar hanya cikin ƙasar nan, Viper ya sani, dodo ya gaya masa, aikin contract rundunar tsaro ta bashi a kanka, kasancewar waccan gwamnati duk gayyar tsiya ce irinka, ya sanya ba su iya yi muku komai ba. Sannan Viper bai shafe shekaru biyar a gidan yari ba, yana can yana karɓar horo na musamman a kan zama cikakken jami'in leƙen asiri. Idan ku kuna amfani da doka, wurin tozarta ƙasa yadda ku ka ga dama, mu ma muna iya amfani da ƙarfinmu ta ɓarauniyar hanya mu yi wa ƙasa aiki. Ina fatan yanzu ka fahimci BODMAS ɗin da Viper ya gaya maka. Kar fa ka zarge shi, sam shi ma wasu abubuwan bai san da su ba, tsuntsu biyu na jefa da dutse ɗaya. Sosai ƙafafuwan Indabo suka fara karkarwa, saboda mamaki da tashin hankali. "Ka hanzarta, ka je ceil ka duba ɗanka, kar wahala ta kashe shi, dan ya saba da hutun da aka samar masa ta hanyar zubar da jinin dubban matasa, a kan harkar daba bayan ka basu miyagun ƙwayoyi, ka gina ɗanka, gashi dai ka bashi ilimin, yana amfanar mutane, gefe guda kuma ya gado duk miyagun halayenka, kuma a haka ka ke ƙoƙarin ɗora shi a kujerar mataimakin gwamna, shi gwamna kai senator, ku cigaba da azabtar da mutane, tun da shi mulkin gadon gidanku ne, you are not serious, Allah yana son bayinsa. Kuma ina tayaka murna, saura wata guda kacal ayi recall election, mutanen yankinka za su yi maka kiranye, abin da ba a taɓa yi a tarihin ƙasar nan ba, sai a kanka" ya ɗauki glass cup ɗin ya bar falon. *** Mamaki ne ya kama Nabila, ganin idon Viper yayi jawur, gidan da ya shiga bai yi kama da na mutanen banza ba, balle ta ce ko shaye-shaye ya shiga yi, hakan ya tabbatar mata da kuka yayi. Ya kama hannunta, ya ja ta zuwa cikin gidan, kasa yi masa magana ta yi, ta cigaba da bin sa. Tijjani da saifu da suke tsakar gida, darewa suka yi, suka ja da baya suna zazzaro ido, ganin wadda Viper ya shigo da ita. Zakiyya kuwa iya ƙarfinta ta saka uban ihu, ta zura da gudu ɗaki, tana dambe da ƙofa taƙi rufuwa, saboda razani da tsoro. Nabila tsaywa tayi tana kallon dattijon, wanda shi ma ya ƙame wuri guda yana kallonta, tun daga sama har ƙasa. Ta baya Nabila ta ji an yi mata wata irin runguma da ƙarfi. Hafsa ce, ta ce "Jauhar, sai da na gaya musu na ganki rannan a asibiti, da na je ganin doctor Abdul yasar, amma suka ce bani da hankali" Jiki a matuƙar sanyaye, Nabila ta rungumeta ita ma, duk da ba ta san wacece ba. Hafsa cikin kuka ta ce "Kin haihu? Ina jaririn naki yake? Mastern ne ya kai ki asibiti? Kin ga aurena ya mutu ko? Na sha wahala a gidan Alhaji mu'azzam". Nabila ta ɗaga kai ta kalli Viper, ta mayar da idonta kan dattijon, amma ta kasa magana, sai lumshe idanunta take yi, tana rufewa tana fatan jin amsar tumulin tambayoyin da ke bakinta, ba tare da ta iya furta ko tambaya ɗaya ba, dan ji take yi, tamkar an kanannaɗe mata harshenta. A tare Major da Nasir suka fito daga mota, cikin ikon Allah suna fitowa, suka yi arba da liti da walid a tsaye a jikin motar da suka zo. Nasir ya ce "Yauwwa Abba gasu nan, ina Viper yake, ina ku ka kai Nabila?" Liti ya ce "Ba a sani ba, kai a wa zaka zo kana yi mana tsawa?" Ya kalli liti ya ce "Ni ka ke gaya wa haka?" "An gaya maka ɗin" Major ya ture Nasir ya ce "Ina 'ya ta take, waye shi yaron a cikin su?" Nasir ya ce "Abokansa ne" "Shi yana ina? Meya kawo mini 'ya nan yayi mata?" Major ya yi maganar a matuƙar hasale. Walid ya ce "Suna cikin gidan can" yayi maganar yana nuna musu gidan da Viper ya shiga da Nabila. Major ya tunkari gidan, liti ya ce "Wallahi bin su zan yi, kar wannan mai kunnuwan ya je yayi musu wani abu" Viper ya ce "Baba wannan ita ce tambayar da na zo maka da ita, nake neman amsarta" A hankali baba ya fara takowa, yana maimaita "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, subhanallah wa bi hamdihi, adada khaliƙihi, wa rida nafsihi, wa zinatu arshih" yana miƙa hannun sa, yana ƙoƙarin taɓa Nabila. Da ƙarfin tsiya, Nabila ta ji an ja ta baya, har ta na ƙoƙarin faɗuwa ƙasa, major ya nuna Baba da ɗan yatsansa ya ce "Kar ka kuskura, baka da wannan ikon, babu wanda ya baka wannan damar, tsohon macuci ma ci amana" A hankali baba ya ce "Yusuf maitama" Major ya ce "Bashir lamiɗo" suka kalli juna. Baba ya ce "Bai kamata haɗuwarmu ta kansace a haka ba" "Babu wani abin kirki da yakamata a tsammata daga azzalumin mutum, mara imani da tausayi irinka, haɗuwar da ta fi wannan muni ita yakamata muyi. Ke kuma wuce mu tafi, da kin san wanenen wannan tsohon najadun da abin da ya aikata wa babarki, da baki yi marmarin ganinsa a rayuwarki ba, wuce mu tafi kafin nayi ƙasa-ƙasa da ke. Kuma da na san kana garin kano, da da nayi retire ban zo kano na zauna ba" Baba ya sha gabansu ya ce "Maitama, babu in da zaka je sai ka gaya mini ita kuma wannan wacece, duk da ko baka faɗa ba, na san 'ya ta ce, amma nauyin laifin da nayi maka bai kai zunubin da aikata mini ba, wacece wannan?" Major ya ce "'ya ta ce ta halak, wadda ba ta da uba, ba ta da wani gata sai na Allah sai nawa, ni ne uwa kuma ki ni ne ubanta, babu uba a tarihin rayuwar ta, na cireka a rayuwarta gaba ɗaya, dan haka kar ka sake saka wa zuciyarka wannan 'yar ka ce". "Amma maitama ka san zan iya shari'a da kai a kan abin da ka aikata mini. Ka san me ka ce mini shekara ashirin da shida da suka wuce" A fusace Major ya ce "Ka daɗe baka yi ba, ni yakamata na yi shari'a da kai, shekaru ashirin da shida baya, bisa cin amana da kisan kai, zan iya cewa kai ka kashe 'yar uwata, dan haka ba abin da zaka tsinana wa rayuwar Nabila, wanda ban yi mata ba" Ƙara Nabila ta saki, ta silale ƙasa, nufarta suka yi gaba ɗaya, Nasir ya durƙusa zai kai hannu kan Nabila, amma Viper ya hankaɗe shi gefe, ya ɗagota. Galala ya buɗe baki, ganin yadda ya kusa kai wa ƙasa saboda hankaɗewar da Viper ya yi masa. Baba ma kan Nabila yayi, amma major ya durƙusa, zai karɓi Nabila daga hannun Viper. Nabila kuwa kanta ne ya juye, wani irin jiri ya ɗebeta, ta faɗi ƙasa, wani irin kuka take yi daga cikin zuciyarta. Viper ya riƙe ta gam, ya kalli major ya ce "Yallaɓai a ganina, kamata yayi ku yi wa Nabila bayanin wacece ita, meyake faruwa, bai kamata ta shiga cikin saɓanin da ku ka samu ba, abu ne da yake a tsakanin ku, da ya faru shekarun da suka gabata. "Wanene kai?" "Mijin ta jikin hoton da na bayar a kai maka". "Mmm mijin wadda ka kashe" major yayi maganar yana kallon idanun Viper. Su Saifu da suka fara leƙowa ɗaya bayan ɗaya cikin tsoro, saifu ya ce "Baba ka yi mana bayani meyake faruwa ne? Mu da kai mun san jauhar ta mutu, to wannan kuma wacece?" *** Chubaɗo tun tana sanya ran dawowar Bashir, har ta fara sarewa, ta fara tunanin ko wani abin ne ya same shi, ba ta iya yi wa kanta komai sai da kyar, saboda nauyi da girman cikin da yake jikinta, abu kaɗan sai haki, gashi babu wanda ta sani a garin, ko ta san wani ma, babu yadda za a yi ta iya magana da su, ita ba yarensu take ji ba. Cikin ta ya shiga wata na tara, ba ta iya cin komai sai dai ta wuni a kwance, salla ce kawai take tayar da ita. Kwanan cikin bakwai da shiga watanni tara, ta fara jin alamun ciwon naƙuda, ga ƙuruciya, gashi ba ta san kan abin ba, dan haka ba ta gane meyake faruwa ba. Ciwo ya ci gaba da ƙaruwa, tamkar zata bar duniya, sai da ta kwana biyu a haka, babu mataimaki sai Allah. Cikin dare abu ya ta'azarra, ta rasa in da zata sanya ranta, tana jin yadda abu ya tokare ƙasan mararta, amma yaƙi fitowa, tayi kukan ma abu ya gagara ta tashi tsaye, ta durƙusa, ta kwanta kowanne ya gagara ta rasa abin da za ta yi ta ji daɗi. Ta ji fitsari ya matseta, ta tafi banɗaki amma ya fara zuba a tsakar gida ashe faya ce ta fashe, ga ta ga banɗakin ta kasa shiga, ƙafafuwan ta suka sage a wurin, dolenta ta durƙusa a wurin, ta fara nishi. Tana jin kan jariri ya fito, amma gangar ciki ta ƙi fitowa, ta yi iya yin ta abu ya gagara, ga numfashinta na ƙoƙarin ɗaukewa, kawai ta nemi wuri ta kwanta daga durƙushen da take, ta zubawa sarautar Allah ido. Ayshercool 08081012143 86 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Wani irin nishi ne ya fara taho mata, ta yinƙura zata tashi, amma ta kasa tashin, tun tana yi kaɗan kaɗan, har ta fara yi da ƙarfi, da tayi wani ƙwaƙƙwara, santaleliyar jaririya ta faɗo jawur da ita, duk da mairamu a galabaice take, haka ta yinƙura, ta tashi zaune, ta kalli jaririyar yadda take ta wutsul-wutsul tana ƙoƙarin yin kuka, amma ruwan da yake fitowa daga bakinta, ya hanata yin kukan yadda yakamata. Ta janyo zaninta, ta fara goge wa jaririyar cikin bakinta, tana kuka yarinyar na kuka, ta rasa yadda za ta yi da ita, ga zaren mabiyiyya a jikinta, bai faɗo ba, gashi ba ma ta san ta yadda zata raba yarinyar da zaren ba, wani irin mugun ɗaurewa, mararta tayi, tare da bayan ta, a take ta fara sabon nishi, ciwo ya dawo sabo, tana tsoron tayi muƙursusu, ta danne jaririyar hannunta, amma da masifa tayi masifa, ajiye yarinyar ta yi a gefe, ta cigaba da jijjiga kanta, jin da gaske wani abu ne yake ƙoƙarin sake fito wa daga jikinta, ya sanya ta tashi ta durƙusa, ga mamakinta wata yarinyar ce ta sake fitowa tare da mabiyiyyar da suke ciki da komai, tayo waje, sai dai ita wannan tana ta tsanyara uban ihu, kamar ana cire mata idanu. Ta zauna da kyar, da zuba musu ido cikin tsananin so da ƙauna take ce wa "Yanzu Allah duk nawa ne wannan? Allah na gode maka, Allah na gode sosai da sosai Allah ka raya mini su duka, ka shirya mini su, duk wannan nawa ne" tayi maganar tana murmushi tana kallonsu, sai dai kuma ta fashe da kuka rashin sanin yadda za ta yi da su. Ƙoƙarin jan jikinta take yi ta tashi, ta ɗauke su, amma abu ya gagara saboda uban jinin da yake zuba daga jikinta. Haka ta koma ta kwanta cikin ƙazantar da haihu a ciki, tun tana ƙoƙarin ɗaukko su, har ta daina gani hankalinta ya gushe. Ba ta da maƙwabta in da take, wani mutum ya wuce ƙofar gidan, ya shiga daji ya yi itace, ya ɗoro a kan keke, da zai wuce ya ji kukan jariri, da ya dawo ma haka. Har zai wuce ya fasa, ya sauka ya tsaya ya hau bubbuga ƙofar gidan, amma shiru, ga kukan yana ji, ɗaya da sauti mai ƙarfi, wani kuma yana tashi kaɗan-kaɗan kamar kukan jaririn mage. Ya gaji da bugu, kawai ya kutsa kai cikin gidan, ja yayi ya tsaya, yana kiran yesu, ganin mace kwance dama-dama a cikin jini ita da yara har biyu ɗanyar haihuwa. Da gudu ya fita nesa da gidan kaɗan, in da yake da mutane, ya tattaro mutane, suka tafi gidan. Sai a lokacin mata suka yanke cibiyar, aka naɗe yaran da ita uwar, aka tafi da su Asibiti. Likitoci suka buƙaci jini, a tsakanin mutanen, suka yi voulanteer suka bayar, aka din ga saka mata, yara kuma aka ce madara, nan ma ba su yi ƙasa a gwiwa ba, aka nemo madarar ba wa yaran, a lokacin duniya na kwance, babu ƙabilanci da gudun taimako. Sai da ta kwana uku a asibiti, ba ta san in da kanta yake ba, dan daga baya jijjiga tayi, bayan an kaita asibitin. Ga yaran aka ce dukansu su biyun, pnuemonia ce da su, dan ta ɗaya har ta fi muni ma, taƙi yin kuka yadda yakamata. Bayan chubaɗo ta farfaɗo, da kyar, ana so ayi magana da ita, babu hali, ita ba ta jin yaren su, su ma kuma ba sa jin nata, gashi sai dai tayi ta bin su da kallo, kamar tana son gane wani abu. Sai da tayi sati biyu a asibitin cif, aka sallameta, suna ta tambayar ta, ina ne gidan su, ina mijinta, amma ba baki sai kuka, har suka fara tunanin ko yaran dakan kuka ne, wato marasa uba. Suka mayar da ita gidanta, suka cigaba da kula da ita, wannan ya kawo mata abinci, wannan ya kawo mata kayan sakawa ita da yaranta, da safe da yamma haka mata suke zuwa, ayi wa yaran wanka, da ruwa mai zafi, sai dai tsakaninta da su ido, sam ba ta jin yarensu, su ma ba sa jin nata. Suka daina damuwa da sai sun san wacece, kawai suka cigaba da hidima da chubaɗo, ta zauna cigaba da jiran Bashir, tana tunanin ko wani abin ne ya tsare shi, ta dawo ta fara jin tsoro ko ya mutu ne a hanya ba ta sani ba, gashi ba ta da kuɗin mota, ba ma ta san hanya ba, balle ta koma gida. Ita kanta ta ƙi lafiya, ga damuwa ga kewar gida ga raino, ba ta san kan abubuwa ba, ga jijjigar da ta yi, ta taɓa mata ƙwaƙwalwa. Kusan duk sati sai an kai yaran nan asibiti, saboda yanayin jikinsu, mussaman ta farkon, duk zuwan matan nan ba sa gane su, sai ta wajen kukansu, ɗayar ba ta da kuzari sosai, amma ita chubaɗo tana kallon abinta take banbance su, ta san wadda ta fara haifa. Sai dai da daddare ta kan ɓuya tayi kuka, dan har da wata dattijuwa, da take tayata kwana, tana tayata kula da jariran. A haka tayi arba'in, a danginta dana Bashir babu wanda ya sani, shi ma kuma a can, matansa babu wadda ta kuma yi masa zancenta, maƙwabta idan sun tambayi matan gidan ina chubaɗo sai su ce musu ta tafi gida haihuwa. Wani mutum ne ya buga ƙofa tare da yin sallama, chubaɗo ta zabura, ta san duk yadda aka yi mai sallamar muslmi ne, ta zari hijjabi ta fita, ta tarar wani abokinsa ne, Tahir, suka gaisa, ya ce "Ya aka yi na ganki a nan? Jiya na haɗu da Bashir, an mayar da shi jigawa har ya cigaba da aiki, kuma na zo nan, na tarar da ke, ke me ki ke yi a nan, gidan nan aka bani, nima nan aka dawo da ni aiki, zan duba abun da babu na gyara" Cikin damuwa ta ce "Au dama yana nan lafiya?" Ya ce "Eh mana, jiya muna tare da shi a jigawa ma" Cikin sanyin jiki ta ce "Dan Allah idan ka koma ka ce ya zo ya tafi da ni, na haihu bani da lafiya" Ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, meyake damun Bashir ne?" Ya shiga ya ga yaran yayi musu addu'a, a haka har suka yi magana da ɗaya daga cikin matan da suke taimaka mata. Cikin takaici, ya ɗauki kuɗi mai yawa ya bata, yayi wa mutanen godiya, ya ce a ranar zai juya, ya je ya samu Bashir, ya ji dalilin sa na aikata wannan rashin mutunci. Sai dai kana naka Allah ya na nasa, a hanya yayi haɗari ya mutu. Jin shiru, har sati biyu, chubaɗo ta tattara yaranta, ta bar garin ba tare da masu kula da ita sun sani ba, ita tana fama da rashin lafiya yaran ma haka, da kurmanci da kwatance, aka kaita tasha, ta din ga cewa Taraba jalingo, aka sakata a mota, ta bayar da kuɗin, a cikin wanda abokin Bashir Tahir ya bata. A galabice ta ƙarasa rigar su, dare ya riga ya yi, tun daga titi da ƙafa har cikin riga, ga yara, suna ta numfashi da kyar, ita ma sai haki take yi ta ƙarasa. Ta je ta tarar da gidansu babu kowa a ciki, ta buɗe ɗakin maitama ta kutsa ciki, ɗakin duk ƙura, haka ta baje yaran suka kwana a ciki, sai wayar gari mutanen garin suka yi suka ga chubaɗo da yara. Ta tambayi ina dadarta, aka ce mata ta mutu, ruwa ne ya tafi da ita, sun je kai amarya ɗaya rigar maƙwabtan su. Ta ƙara kiɗimewa, halin da take ciki ya ƙara ta'azzara, jikinta ya ƙara rikicewa. Ga yara babu lafiya, kamar almajira, haka ta cigaba da rayuwa a gidan itakaiɗai, sai dai a shanunsu, da suke wurin baban su bello, ɗan uwan baffa, ana bata madara, idan sun yi tuwo suna bata ko kunu. Ba yadda ba su yi da ita ba, suka tambayeta yaya ina auren ba, ta dawo riga ta zauna, amma taƙi faɗa. Yan garin suka din ga zunɗenta, wai kwaɗayi ne da zunubin Jibo, duk ya janyo mata. Yara maimakon su din ga girma, sai suka din ga yanƙwanewa, duk suka lalace kamar yaran aljanu, gashi wasu lokutan tayi ta shirme, ba ta iya gane meyake faruwa saboda jijjigar da tayi, gashi kullum cikin haki take, ga jego kuma babu cikakkiyar kulawa. Yara kuwa kullum cikin amai da gudawa suke, da tari da sarƙewar numfashi, sai dai a basu jiƙe-jiƙe da hayaƙi, aikuwa suka ci-gaba da tsula gudawa ba ƙaƙƙautawa. Sai da suka yi wata biyar, kwatsam Allah ya kawo maitama garin, dan shi kansa bai san da mutuwar ramata ba, sayayya yayi ya zo ya gaisheta, dan duk da baffa ya rasu, ba zai manta da alkhairi da kuma hidimar da tayi da chubaɗo ba. Ya shafe watanni baya ƙasar, an tura su yaƙi can libiya, dan matansa ma sun fara tunanin ko an kashe shi a can, shiyasa bai samu ya je yaga chubaɗo ba, fatansa dama daga nan jalingo ya kwana biyu ya tafi Bauchi ya ga Chubaɗo. Sai dai abin da ya tarar ya ɗaga masa hankali, mairamu ta koma baƙa, da ta ganshi ma sai da ta ɗan yi shiru sannan ta tuna shi. "Mairamu shi Bashir ɗin ne ya turo ki riga ki zo ki yi jego?" Ta girgiza masa kai. "Ki yi mini bayanin, menene ya faru, kan na zane ki" Cikin rawar murya, ta gaya masa komai tiryan-tiryan, ba ƙaramin mamaki ne ya kama shi ba, abin kamar almara ya din ga tunanin anya Bashir yana hayyacinsa. Ya ɗauketa da yaran ya nemi a garin wata ta raka su asibiti, dan ya san za a kwantar da su, amma aka rasa mai yadda, ya ɗauke su zuwa asibiti, sai dai kwananta biyu a asibitin, aka tura su Gombe, saboda zuciyarta ta taɓu, tun lokacin tana da ciki. Ya sha faɗa sosai a wurin ma'aikatan lafiyan, suka din ga cewa a haka kamar yana da ilimi amma yayi wannan shirmen, aka yi sake tamowa ta kama yara ƙanana, ita kanta uwar yunwa ce a jikinta, ga complication na jijjiga da suka gano, bayan sun yi mata tambayoyi, ga kuma zuciya ta taɓu. Shi dai bai ce komai ba, aka basu kwanciya. Shi ne yake kwana da chubaɗo, da taimakon nurses yake kula da ita, suka ce lallai ya samo mata mace, jinya dole sai da mace. Ya rasa yadda zai yi, ya koma garin da ya fara karatu, su sun samu cigaba sosai, ya ce a samo masa wadda zata yi masa jiyyar ƙanwarsa ya biyata, aka samu wata 'yar dagaci, da aurenta ya mutu mai suna magajiya, ta ce ita ko kyauta za ta yi, ba ta manta ɗawainiyar da ya din ga yi da mahaifinsu ba. A haka ya daddafa, ya koma can gidansa, ya sanar da matansa abin da yake faruwa, Allah ya sauwwaƙe kawai suka yi masa, ba tare da wata tayi karar bin sa ta duba mairamu ba. Ya ɗaukko babban ɗansa Nasir, ya taho da shi,  ya zo ya duba mairamu, da jariranta, da suka yi masa kyau a ido duk da ba su da lafiya. Abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, ɗayar kamar ba zata yi rai ba, ga shi chubaɗo na fama da kanta, ga rainon yara marasa lafiya. Suka wayi gari ɗaya ko numfashi ba ta iya yi, aka saka mata oxygen, ƙarin ruwa sai da aka aske mata gashin kanta, sannan aka saka, jininta ma da za'yi gwaji, ta mararta aka samu jinin. Aka bawa maitama ɗayar aka ce ya kaita wani asibiti, ita ma a saka mata oxygen nan space ya ƙare, ita ma kuma tana buƙata. Yana tafe a mota, baƙin ciki da takaicin abin da bashir yayi masa ya hana shi sukuni, kamar ya jefa yarinyar ta taga, gaba ɗaya ya ji haushin yaran yake ji, ya din ga dana sanin rashin jin maganar baffa. Kawai zuciya ta ɗebe shi, ya canza akalar motarsa, ya nufi Bauchi. Yana tafe a hanya, yarinyar babu kuka, babu komai, sai shan hannunta da take yi, duk da tana ta haki. Bai manta ba haka uwar ma aka yi ta fama da tana jaririya, amma aka ƙi kaita Asibiti. Yana tuƙi yana yi yana kallonta, tayi bacci ta tashi, ta sha hannunta, ko uffan sai da ya tsaya ya sai ruwa ya bata. Saboda tsabar masifa da wahala, yaran da ya kai su fara zama, amma suna kwance duk yunwa da zawo ya cinye su. Ya ja tsaki a fili. Har ƙofar gidan ya isa, cikin matsananciyar sa'a, da ya aika aka yi masa sallama da Bashir ya ga ya fito yana gari, sai da ya ga maitama, sannan ya tuna da wata halitta wai ita mairamu. "Ka bani kunya ka bani mamaki Bashir, meye ribar abin da ka aikata ka wulaƙanta mini 'yar uwa, ka tozarta ta? ta haihu a wulaƙance, ka ci amanata, amma na bar ka da Allah, ga wannan nan, ita ce mai alamar zata rayu shima wataƙila, yar ka ce na kawo maka, yar uwata ba zata mutu tana yi maka wahala kana gefe ba, kana tsula rashin mutunci. Kuma, ka gaya mini menene matsayar aurenku a yanzu? Tun da ta ce baka saketa ba" Bashir ya kalli maitama, ya kalli yarinyar da take ta bacci, ya ce "Na saki mairamu, Saki ɗaya Allah ya haɗa kowa da rabonsa, 'ya ta kuma na karɓa Allah ya raya mini" Cikin tashin hankali ya kalli Bashir ya ce "Ka saketa, ba sakin ne ya bani haushi ba, amma laifin me tayi maka?" Bashir ya girgiza kai alamar babu. Maitama ya haɗiye yawu mai matuƙar zafi da ɗaci, ya so ya sanar masa yaran biyu ne, amma sai ya kasa saboda tsananin mamaki. Kuma ya san wadda ya baro, wannan yarinyar kafin ya koma ta rasu, saboda ta galabaita da yawa, dan haka ya ga babu amfani gaya masa, ya ce "Na gode Bashir da wannan tukuici, ya taka ce dama, an bar maka halak malak, zan nesan ta ka da mairamu nesantawa ta har abada, kuma in sha Allah duk wani sukuni da nutsuwa da ake samu da walwala a sanadin aure ba zaka same shi ba, kai da Allah da ni da zuriyarmu ba zaka sake ganin ire-iren mu ba, in sha Allah zamu ƙaddara babu wata alaƙa, ko wani abu da ya jiɓanceka a rayuwarmu" A hankli yarinyar ta buɗe idanunta, ta ƙura wa maitama, sai kuma ta wangale masa dadashinta tana dariya, tare da jan numfashin ta da kyar. Maitama ya juya ya nufi motarsa, yana jin tamkar ya fasa ihu, Bashir kuwa ji yayi sakin mairamu kamar ya saukewa kansa wani nauyi ne, ya shiga da yarinyar gida, cike da ƙaunarta. Bashir yana tafe a mota, kawai tausayin mairamu ya lulluɓe shi, sai kuma ya din ga tunanin da ya sani, bai ɗauki yarinyar nan ya bashi ba, ita menene laifinta, dariyar nan da ta yi masa, sai ta tsaye masa a ƙirjinsa, ya kasa mantawa, ganin ita ma a galabaicen take, ya sanya ya din ga addu'a Allah ya sa yarinyar ta mutu, dukkansu ma su mutu kowa ya rasa, shikenan babu sauran alaƙa a tsakanin sa da Bashir. Yana komawa da daddare, aka din ga tambayarsa ina Husna take, ya jikinta, dan dama Hassana da hussaina kawai ake ce musu, a asibitin, ta ce ba ta san sunan su ba. Dan ita wannan yaran kawai take cewa, kasancewar su yaran fari. Mairamu na kan gado na fama da ƙarin jini, ta ji nurses na tambayar "Ya jikin haussaina" Mairamu ta ce "A'a, ba ita ba ce, babbar ce ya tafi da ita, ƙaramar tana nan" "Allah ya yi mata rasuwa a hanya, har an binneta ma, shiyasa ban dawo da wuri ba" Duk da ƙirjinta ya buga da ƙarfi, amma ta dake, a matsayin ta na bafulatana, bai kamata ta nuna damuwa a kan ɗan fari ba. Maitama ya sha mamaki, da ya ga jaririyar da ya bari ta fara farfaɗowa, bai taɓa tunanin zata ƙara mintuna talatin ba ta mutu ba. Da an tambayi ranar da aka haife su, nawa ga wata, sai mairamu ta ce ba ta sani ba, ita dai ta san ranar arfa ne. Maitama ya tambayeta, ainihin sunan da za a saka wa jaririyar. Ta ce duk sunan da ya saka shikenan, kasancewar yana son sunan Nabila, sai ya saka mata Nabila, ya ce "Tun da ranar arfa aka haife ta bari mu saka mata sunan 'yan gayu, arfa" Tsananin tausayin Nabila da wahalar da ta sha, ya sanya ya fara yi mata wata irin soyayya, da fari ba dan tafi jigata ba, ya so ace ya haɗa har ita ya kai wa uban su, shi ya kula da ƙanwarsa, tun da ba shi da mutunci, amma idan ya tuna yadda yarinyar da ya baro, ta kalleshi har da ƙarfin hali dariya, sai ya ji babu daɗi a ransa. Hutunsa ya riga ya ƙare, dan haka ya ɗauki chubaɗo, ya tafi da su illori, in da yake aiki a lokacin. Ya mayar da ita asibitin sojoji, sai dai ya lura da yadda idan chubaɗo ta zauna take yawan shiru, ta saka damuwa a ranta sosai. Cikin kulawa ya ce "Mairamu, ke da ake fatan ki samu lafiya, menene kuma na tunani da saka damuwa a rau?" Ta ce "Bakomai, yarinyar nan har ta mutu, babanta bai taɓa ganinta ba, ina ga ko shi ma mutuwa yayi ba a sani ba" duk tsananin kunya irin ta ta, hakan ya tabattar masa da damuwar rashin 'yar ta ne da kewar mijinta yake damunta, haka yayi ta rarrashinta, ƙasan zuciyarsa yana jin, ba zai iya yafe wa Bashir ba. Aka sallame su, suka koma gida, baba magajiya ke yi wa arfa komai, da taimakon Nasir, da kullum yana liƙe da arfa, yana raino. Sai a lokacin ya yi wa Nabila hakika, sai dai an hana mairamu cin jan nama a lokacin. Yayi mata suturu, ya yi wa Nabila kayan sakawa masu kyau na zamani. Sai da babar Nasir ta magantu a kan "Wai dan Allah ina uban yarinyar nan, da ka ke ta wahala, tun da ka dawo da su, bai zo ya duba ta ba, ai hakkinsa ne" Ya bata amsa da ba ta da uba, ni ne uban. Can Bauchi kuwa, Bashir matansa sai ganinsa suka yi da jaririya, suka tambaye shi wannan ƙarmasashiyar 'yar fa a ina ya samo ta. "'yar wurin waccan yarinyar ce, yanzu yayanta ya kawo mini ita, dan ya tura mini takaici, ni nama manta da ita gaba ɗaya, na karɓi kayata ina son abata". "To kai ya zaka yi da jaririya, saboda rashin mutunci da zalunci, sai a ɗaukko wannan yar mitsitsiyar yarinyar, duk a tsotse ta kusa mutuwa a kawo maka, kai amma mairamu azzaluma ce, kalli ƙashin haƙarƙarin yarinyar, kamar fara sai uban fari da gashi kamar horo". Ya sake gyara ta a cikin zani, ya kalli Zakiyya ya ce "Zakiyya, ko ke zaki shayar da ita, tun da kin ga shayarwa ki ke yi" Ta buga tsalle ta ce "Wallahi ba zata ba wa 'yar mayu nononta ba, wannan yarinyar abar tsoro, ta tsotse mini jini a banza, wallahi ba zan bayar ba" Uwargidan ta ce "Dama ni ban haihu kwanan nan ba, dan haka bani da abun bata, ban da jakanci irin na mutumin daji, kawai ku wofantar da jaririya haka, Allah wadaran naka ya lalace" Ƙarshe sai azare ya koma, aka kaita Asibiti, aka lalubi mai shayarwa a dangi, sai dai danginsa ba ƙaramin zagi suka yi wa su chubaɗo ba, bayan da ya gaya musu rabuwa suka yi aka dawo da yarinyar. Wadda ta karɓi 'yar ta ce 'Kai kuwa basiru, me yarinyar nan tayi maka, ka saketa? Duk haƙurinta da biyayyarta" yayi shiru, dan shi kansa ba shi da amsar tambayar da ta yi masa. Illori, arfa ta murmure tsaf, idan maitama yana yi mata wasa, yayi ta ce mata gawa taƙi rami, chubaɗo ta gaji, ta ce wa magajiya, dan Allah ta ce wa hammanta, ko za aje a duba ko baban yaran mutuwa yayi, ko wani abin ne ya same shi. Da ta gaya masa, sai ce mata yayi babu buƙatar hakan, dan ba zai iya kallon mairamu, ya bata saƙon sakin da Bashir yayi mata ba. Har Arfa tayi watanni tara, mairamu na jinya, matan maitama suka ɗora mata tsana, baya ta tasu sam, komai chubaɗo komai ita, magajiya kuwa ta ji daɗin zama, ta zauna tare da su, ta ci-gaba da rainon Nabila cikin soyayya da ƙauna. Dare ɗaya chubaɗo ta tashi numfashi ya sarƙe, suka ɗiba suka yi asibiti, kwananta biyu a asibiti ta daina magana, ta kasa tashi. Hankalin maitama ya ƙi kwanciya, ya rasa abin da yake yi masa daɗi, ya rikice ya kasa zaune ya kasa tsaye. Kwana na biyar, ya zo dubata, ta buɗe idonta, ta kalle shi, ta miƙa masa hannu, ya kama hannun nata, ya durƙusa a gaban ta, ta ce "Nabila" karon farko da ta kira sunanta. Sai kuma ta sake ce wa "Bashir" shi ma karon farko da ta kira sunan sa a rayuwarta, "Allah ya sa 'ya ta ta samu lafiya, ka ɗaukko mini ita" A hankali ta lumshe idanunta, ya zata bacci tayi, ashe tafiyar kenan. Ga shi namiji, ga shi soja, amma ya kasa jarumta, ya rikice tamkar hankalinsa zai gushe, ya ji mutuwar chubaɗo, fiye da yadda ya ji mutuwar iyayensa. Bayan rasuwar ta, ya yi niyyar sallamar magajiya, amma matan suka nuna masa ba zasu riƙe Nabila ba, kai tsaye babar Nasir ya fara danƙarawa saki, baba magajiya ta yi ta bashi haƙuri, ta ce zata ci gaba da zama ta kula da Nabila. Bayan wani lokaci ya haɗu da wani ɗan garin su Bashir, yake gaya masa ai kwanaki wata 'yar wurinsa mara lafiya ma ta rasu, hakan ya saka maitama zata ko jaririyar nan ce, amma yar wurin zakiyya ce da take shayarwa taƙi haɗawa da Nabila, ta mutu. Ya ƙallafa soyayyar Nabila a ransa, gani yake yi tamkar chubaɗo ce, ga pneumonia ta koma mata Asma, bai yi mamaki ba, dan dama larurar mairamu ce. Hakan ya ƙara sanya wa yake kaffa-kaffa da ita. Gashi saboda yawo tsakanin dazuzzukan barrack a garuruwa, da maitama yake yawo da su saboda wurin aiki, Nabila ta kwashi aljanu, dan dama ba ta jin magana ko kaɗan, hakan ya ƙara mata baƙin jini a gidan, gashi ba ta taɓuwa. fitinar Nabila ta mussaman ce, saboda larurarta, ga tsalle-tsalle, da iface-iface da an taɓa ta ba wuya ta faɗi, ko kuma asma ta tashi. Ba ta aikin fari balle na baƙi. Da ta isa shiga secondary school, ta ce ita boarding take so, babu yadda maitama bai yi da ita ba, ta dage ta ce ita sai boarding. Haka aka kaita boarding jss1 cikin ƙedaren arna ƙabilu, a ajinsu ta haɗu da sumayya, ita kaɗaice bahaushiya musulma. sai ya sanar musu larurarta, saboda kar a samu matsala. Da farko faɗa suka fara yi, daga baya ya zama ƙawance, sumayya ba ta da hayaniya, Nabila kuwa akwai fitina da neman magana. Mahaifinta ya rasu, coustom ne a hatsarin mota, wan mahaifinta ne ya kawo ta boarding, idan aka yi hutu kamar kar su rabu, Sumayya a mayar da ita Kano, Nabila kuma tana nan garin su na Bayelsa lokacin, Maitama ya zama major. Ya saba da ƙanin mahaifin Sumayya, wataran idan hutunsu ba yawa, a gidan su Nabila take zama, komai tare yake yi musu. A makarantar akwai tsirarun musulmai, da malamin da yake kai koyar da su ilimin addini. Idan an yi hutu ma, akwai malamin da yake zuwa gida, koyar da Nabila karatu. Nabila ta ce ita ma soja take son zama, Abba ya ce ba ta isa ba, har kuka ta yi, wai ita a lallai sai ta zama soja, ga samarin inyamuran nan, suka yi mata caaa lokacin da ta zama budurwa. Abba ya ce ba zata yi soja ba, ta ce law zata yi. Suka haɗa kai da sumayya, wai Benin zasu tafi jami'a, Abba ya ce bai yarda ba, saboda ba ta da cikakkiyar lafiya. Tun suna sakandare idan ciwo ya tayar wa Nabila, sumayya ce take jinyarta. Ganin ya hanata zama soja, yanzu kuma ta kawo issue na ga makarantar da take so, ya ƙyaleta, ita ma sumayya ɗan uwan babanta yana ta ƙoƙari, ya ce sumayya ba zata je Benin ba, major ya lallaɓa shi, ya ce su yi musu addu'a. Ɓangaren Bashir kuwa, jaririyar sa ya saka mata fatima jauhar, kamar ba shi da wata 'ya sai ita, Allah ya jarrabe shi da son yarinyar nan. Ana yayeta ya je ya ɗaukko ta, cike da makirci, mama ta karɓa ta ce ita zata riƙe, saboda ta ƙara samun fada a wurinsa, dan kuwa ya ƙara samun rufin asiri lokacin, dan sun koma kano ma, yana ƙoƙarin barin aiki ma. Bawa aiki da kasuwanci muhimmanci, haɗi da sakaci da ibada, sallolin farilla kawai ake samun yi, babu azkar da neman tsari, hakan ya sanya matan Bashir samun damar ci gaba da yi masa asiri, kowacce so take ace babu ya ita. A ƙarƙashin zuciyarsa yake jin wani irin nauyi a cikin zuciyarsa, kamar akwai wani babban bashi a kansa, da yakamata ace ya sauke, amma ya rasa menene. Bashir yayi aure-aure, amma su zakiyya na hana su zama, su kansu mugunta suke yi wa kansu, amma sun kasa galaba a kan junansu. A wayance, tun jauhar tana ƙaramar yarinya, take fuskantar izaya kala-kala, amma Bashir ba ya iya magana, duk da yana matuƙar tausayin jauhar. Bai taɓa zancen kaita wurin babarta ba, ko kaita garin su ba, sai dai hoton ta, da ya nuna mata. Nabila ta kammala makaranta, jin zasu koma kano, kamar ta taka rawa, dan tana tunanin rabuwa da Sumayya, saboda shaƙuwar da take tsakanin su. A Kano tayi bautar ƙasa, ta fara aiki, duk da ba wani zama take a gidan major ba, ta tashi ana nuna mata ƙiyayya muraran a gidan, daga baya ta fuskanci major ba shi ya haifeta ba, dan haka ta saka shi a gaba, da tambayar ina babanta, tun da ya ce mamanta ta mutu, sai dai ta kan fuskanci mummunan ɓacin rai, a duk lokacin da ta tambaye shi. Tun tana yarinya, major ya gargaɗi Magajiya da Nasir, a kan kar a kuskura, Nabila ta san cewa su biyu aka haifa, duk da ya samu labarin mutuwar ɗayar, kuma yayi mummunan gargaɗi a kan yi wa Nabila duk wani zance da ya danganci mahaifinta, domin ya yanke duk wata alaƙa tsakaninta da mahaifinta har abada. Ta na yawan mafarki da wata mai kama da irinta sak suna wasa tare tun tana yarinya, idan ta farka tana jin tsananin ƙaunar yarinyar da suke wasan tare, idan ta gaya wa baba magajiya, sai ta ce mata shirmen mafarki ne da iskokanta. Sai dai daga baya ta daina mafarki da ita, daga baya kuma bayan ta girma sosai, ta cigaba da mafarkinta, har cikin zuciyarta take jin matsananciyar ƙaunar wadda take gani a baccin nata. Sai dai yadda take ganinta daga baya bayan ta girma, cikin damuwa take ganinta, tana nuna mata inuwar wani mutum a cikin sarƙa. Ta samu baba magajiya ta ce "Wai ni baba anya ba 'yan biyu ba ce ba? Yarinyar da nake mafarki ba ta girma ta zama kamar ni". "A'a yan dozen ne ba biyu ba, gane-ganenki ne na makaran kanki, suke buɗe miki ido, dama ai tun kina yarinya ki ke yi" ta shiriritar da maganar. Wataran suna camp, ta sake mafarki da yarinyar, tana kuka tana nun mata na cikin sarƙar, ta farka a razane sai ta ji kamar muryarta a zahiri tana kiran sunanta "Nabila" tsakiyar dare ta tashi zata fita, aka riƙeta da kyar. Ta daina mafarkin mai kama da ita, sai inuwar wannan mutumin a cikin sarƙa, da take gani babu yau babu gobe a cikin baccinta. Da kyar Nabila ta kalli Viper, ta na suffanto inuwar wanda take gani a cikin bacci. Motsa bakinta take yi, tana son tayi magana, amma ta kasa ta ɗago hannunta da kyar tana nuna Viper, amma bakinta ya hau karkarwa. Ayshercool 08081012143 87 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Bakin Nabila ya cigaba da karkarwa, idanunta suka fara ƙoƙarin kakkafewa. Liti ya na tsaye daga baya a jikin bishiyar umbrella da take tsakar gidan, wani irin tausayin Nabila da jauhar har ma da Viper ya mamaye shi, har gara ma Viper, shi yanzu idan da sabo ya riga ya saba, ita kuwa an rabata da 'yat uwatta, an nesanta su da juna, kuma ta rasu ba su haɗu ba, sosai ya ji nadamar abubuwan da ya din ga yi wa Nabila. A hankali Viper yake ɗan girgizata, yana kiran sunanta "Nabila, me yake damunki?" Su Zakiyya da suke ɗaki kuwa, gaba ɗaya suka yi sak, dan sun san su ne kanwa uwar gamin abin da ya faru. Baba ya miƙe hannu zai taɓa Nabila, major ya riƙe hannunsa ya ce "Bashir, haryanzu ina nan a kan bakana, babu kai babu abin da mairamu ta bari, ba zan taɓa baka Nabila ba, kuma ka cire a ranka Nabila ba 'yar ka ba ce ba" "Yanzu maitama abin da ka yi kana ganin daidai ne? Baka gaya mini yarana biyu ba, ka kawo mini ɗaya ka nesanta ni da ɗaya? Zan iya ƙararka fa a kan abin da ka yi mini" "Shut up! Ko kuma ni na yi ƙararka ba, da ka kashe mini 'yar uwa, ai dai na kawo maka ɗayar ko, ka aura wa ɗan daba ya kasheta, kai ka sani" Viper ya yinƙura da Nabila a hannunsa, sai wata irin miƙa take yi, ya nufi waje da ita. Bayansa suka biyo, Bashir sai share hawaye yake yana kiran "Aminu ina zaka kaita ka tsaya na ga 'ya ta". Cikin ɗaga murya, major yake yi wa Viper magana, a kan ya tsaya, Nasir kuwa kasa shan gaban Viper ya yi, gaba ɗaya suka bi shi. Sojan da ya kawo su, yana ganin Viper ya fito, ya buɗe masa mota, ya saka Nabila a ciki. Saifu ya riƙe shi ya ce "Ina zaka kaita, dole fa ka tsaya a gama wannan tarzomar" "Cika ni" Viper ya yi maganar yana kallon saifu. Saifu ya cika shi ya ja da baya. Viper ya kalle su ya ce "Zan mayar da ita asibitin barrack, idan na bar muku ita a nan, zan iya yin laifi tun da tana ƙarƙashin kulawar jami'an tsaro ne. Walid taho mu yi gaba, su taho tare da liti" "A'a shi dai su taho tare" Zakiyya ta ce "To a tafi babu wata mace, mu tafi gaba ɗaya mana" kafin Viper ya bata amsa, Hafsa ta ture shi, ta shige cikin motar, yanayin yadda ta shiga kawai zaka gane kan babu daɗi. Ya kalli saifu ya ce "Ka shiga ka riƙeta mu tafi" Hafsa ta ƙanƙame Nabila, tana kuka ta ce "Yaya saifu, rannan ba ce muku naga Jauhar a asibiti ba, aka ce bani da hankali, to ai gashi yanzu ta dawo ba ta mutu ba" Walid da Viper suna gaban mota, sai da Walid ya waiwayo gwanin ban tausayi, bai manta hafsa a da ba, yar gayu 'yar ƙwalisa, jawur da ita ta sha mai, amma yanzu duk ta koma baƙa ta firgice. Har suka isa barrack, Nabila tana wannan miƙar bakinta yana rawa, viper ya ce a ƙarasa da su asibitin sojoji, saifu ya ce "Anya wannan abun ba aljanu ba ne?" "Ba wani aljan" Viper ya faɗa a daƙile. Sai dai suna isa, aka ɗauki Nabila aka shiga da ita, Viper ya yi wa ma'aikatan alama, da karba bari kowa ya shiga in da take. Tafiya ce mai nisa sosai, daga gidan baban Nabila zuwa asibiti, amma har suka zo, jikinta a sandare yake, dai dai idan ta motsa tayi miƙa kawai. Alluran bacci kawai aka yi mata, sai drip na babu gaira babu dalili, kusan ko ina a jijiyoyin hannunta akwai tabon hudar cannula. Major ya fara tambayar ina aka kai masa 'ya, aka ce masa an hana kowa ya shiga in da take. Cikin hasala ya ce shi ma fa tsohon ma'aikaci ne kamar yadda yake gaya musu, dan me za ace ba zai shiga ba. Aka ce masa ba bisa umarnin sojoji aka hana kowa shiga wurinta ba, bisa ga umarnin likitoci ne. Baba ma ya ƙarasa tare da tijjani, yana kiran wayar saifu, dan ya gaya musu, a in da aka kwantar da Nabila, bayan su haɗu, saifu ya sanar masa an hana kowa shiga. Baba bai damu da irin mugun kallon tsanar da major yake yi masa ba, babban burinsa kawai ya sake tozali da kyakywar fuskar 'yar sa, mai kama da jauhar Waliyiyya, kuma kamannin mairamu chubaɗo. Walid ya kalli liti, da kamar ya koma kamar ɗan tsakon da ya faɗa ruwa, duk yayi tsuruu da shi, kamar mara gaskiya. "Ya dai liti?" "Walid zuciya da saurin fushi ba su yi ba" "Meyafaru?" "Yarinyar nan wani irin mugun tausayi ta bani, wallahi kamar na yi kuka, tabbas na daɗe da gane ba ita ce jauhar ba, tun da damu aka yi jana'izar ta, hausin abin da wancan banzan yayi mini mai ƙugu kamar an miƙo kare ta taga, da rashin kunyarta da shishishigi da take yi wa Viper, ya sanya na ji na tsaneta, haka kurum idan yana saurarenta, sai na ji kamar ya na cin amanar jauhar ne, ko bayan mutuwar ta, bai kamata ya kula wata mace ba" "Abin da nayi ta nuna maka kenan liti, amma ka ƙi ganewa, kullum cikin yi mata rashin mutunci ka ke, ji maganganun da ka caɓa mata muna tafe a hanya. Ai a duniya idan zaka yi ƙiyayya ka yi ta sama-sama haka ma soyayya amma kawai ka je ka yi ta hantararta, ashe abin da yayi jauhar shi ya yi Nabila" "Amma kamar su ta yi mugun ɓaci fa, ni fa na daɗe ina kokwanton idan ba fatalwar jauhar ba ce, halayensu da na din ga nazarta na fuskanci wannan sai a hankali, gaba ɗaya sun sha banban ta fuskar halayya, amma hatta muryarsu iri ɗaya, sai dai ta jauhar ta fi sanyi da nutsuwa, wannan kuwa tsabar tsiwa da masifa ce a cikin ta ta muryar, Allah sarki Allah ya jiƙan 'yar madara". Walid ya amsa da Amin. Major kuwa ganin Bashir ya kafe ya nace, ya sanya ya Kalle shi ya ce "Bashir, ka kama hanyarka ka bar wurin nan, wallahi ko me zaka yi, ba zan ba ka Nabila ba, kar ma ka yi tunanin ayyana kanka a matsayin mahaifinta" "Maitama babu in da zan je, har sai ya ta ta farfaɗo, kuma sai ka bani kayata na tafi da ita" "Ita ma ka je ka aurawa ɗan daba ya kasheta kenan" Bashir ya ce "Ko ma wa zan aurawa, 'ya ta ce, ina da iko a kan aba ta" Saifu ne ya din ga ba su haƙuri, a kan su yi haƙuri su daina abin da suke yi. Viper kuwa yana zaune a cikin ɗakin, da take tana bacci, yayi alwala ya gabatar da salla, sannan ya nemi wuri ya zauna yana danna wayarsa. Ya ɗago ya kalleta jin ta yi tari, bacci take yi, amma yanayin fuskarta ya nuna ba daɗin baccin take ji ba sam. Sosai Nabila take kama da jauhar, babu yadda za ayi ka ce ba mutum ɗaya ba ce ba, sai ka rayu da jauhar, ka dawo ka rayu da Nabila, zaka fuskanci su na da banbanci. Amma mafi yawa they have so many things in common. Ya mayar da kansa kan wayarsa, ya ci gaba da daddanawa, bai fargaba kawai ya ga ta tashi tsaye, ta fizge ƙarin ruwan, jini yana zubowa daga hannunta. Da azama ya tashi, ganin idanunta a rufe ko gani ba ta yi, ta nufi hanyar fita daga ɗakin. Shan gabanta ya yi ya ce "Ina zaki je?" Da kyar ta buɗe rinannun idanunta ta kalle shi, ta je uban tsaki, ta raɓa shi za ta wuce, amma ya riƙe ta, ya danne hannunta da yake zubar da jini. Ya ce "Abla, menene? Meyake damunki?" Ta tsaya ƙyam sai rangaji take yi kamar wadda ta sha ta bugu, tana lumshe idanunta ta na buɗe su. "Abla" ya sake kiranta a hankali. Kamar wadda ta farka daga bacci ta kalle shi, ta ce "Mafarki ne ko, ai ba gaske ba ne ko?" Kan ya kai ga ba ta amsa, ta kalli kayan jikinsa, ta kalli na ta, ta shafa fuskarta, ai sai ta saka kuka, ta fara kiran Abba da ƙarfi, tana ƙoƙarin ture Viper tayi waje. "Shikenan, ya isa ki nutusu, bari ayi masa magana ya shigo ki ganshi, amma mu je ki zauna tukuna" kamar mahaukaciya sabon kamu, haka Nabila ta din ga misbehaving. Viper ya yi waya, ya ce a ba su damar su shigo su ganta. Sai ga su duk sun shigo, ga hafsa saifu da Tijjani, major da Bashir na rige-rigen shigowa, sai kuma su liti da walid da Nasir. Bin su ta din ga yi da kallo, Hafsa ta ƙarasa gaban gadon Nabila ta ce "Waliyiyya, sannu kin tashi? Ina ɗan jaririnki yake? Shikenan yau sai ki koma gidan Master, ku ci gaba da shan soyayya" ƙuri Nabila ta yi mata da ido, dan ba ta santa ba sai a ɗazu ta taɓa ganinta. Major ya ce "Arfa, ya jikin naki?" Tayi shiru ta sunkuyar da kai. "Arfa Abba ne fa, ba ki gane ni ba ne?" Bashir ya zagaya ta gefenta, yana ƙare mata kallo, cikin matsananciyar soyayya da ƙauna. "Yarinyata, ki kalle ni, ni ne mahaifinki" yayi maganar cikin matsanancin rauni. Nabila ta ɗaga kai, ta kalle shi sau ɗaya, ta kawar da kanta, tabbas ta ɗokanta da son ganin mahaifinta, ba irin alwashin da ba ta yi ba, na idan Allah ya sa yana raye, su ka haɗu, babu ruwanta da Al'ada sai ta rungume shi, ko a yaya yake, sai dai kash! Ba ta ji daɗin a yadda mahaifin na ta ya kasance ba, duk da ba ta san mahaifiyarta ba, amma uwa uwa ce, ba ta ji daɗin abin da ta ji game da tarihin zaman su ba. Nasir ya ce "Nabila, ki yi magana mana" Major ya sake cewa "Arfa, ki kalle ni mana? Meyake damunki?" "Ni ku daina nuna ku na so na, ba kwa so na ba kwa ƙaunata, meyasa za ku yi mini haka? Ni menene laifina a tsakanin ku? Ace ina da 'yar uwa ban ganta ba, ba ta ganni ba har ta koma ga Allah, kun san me nake ji kuwa? Ban san uwata ba, 'yar uwata kuma ta mutu ban taɓa ganinta ba, duk ba kwa so na, kun fifita tsamin alaƙar ku a kai na, ta mutu fa ba zan ganta ba kenan. Abba tsananin son da ka ke yi wa 'yar uwakka ya sanya ka yanke wannan hukunci, ni yanzu ba ka yi tunanin a wane halin nake ciki ba, da na rayu kamar wata mujiya, ba wani ɗan uwa da zan ɗaga in kalla ya na so na tsakani da Allah" tayi maganar tana wani irin kuka mai matuƙar sauti. "Shikenan da ban haɗu da Viper ba, ba zan san ina da 'yar uwa ba, Abba ka ɓoye mini, kai kuma babana, duk burin da na ci na in ganka, gwiwata ta yi sanyi, meyasa ka yi wa mahaifiyarmu haka, da ba ka yi haka ba, da babu lallai a raba ni da 'yar uwata, ban fa taɓa ganinta ba, shikenan ta tafi har abada" Ta miƙe tsaye a kan gadon, tana neman hanyar sauka. Viper ya ce "Meye haka ne ki ke yi? Ina kuma zaki je?" "Ka kira mini sumayya dan Allah" tayi maganar cikin sigar magiya. "Sumayya kuma? Me za ta yi miki?" "Ni dai ka kirawo mini ita" "Magariba ta yi, ba za a kirata ba sai da safe" Likita ne ya dawo, ya ce duk a fita a ƙyaleta, a stage ɗin nan da take, za ta iya samun matsalar ƙwaƙwalwa, a ƙyaleta ta huta. Matsananciyar nadama da jin kunya, suka mamaye Bashir yanzu shikenan Nabila ba ta farincikin ganinsa. Shi ma major, damuwa ce ta mamaye ilahirin fuskarsa, wani irin dana sani yake yi, na raba Nabila da jauhar da ya yi, wato duk wayon bawa ƙaddara ta riga fata. *** Gidan su jauhar, tun bayan da Zakiyya ta yaudari maman saifu, ta aurawa Alhaji mu'azzam Hafsa, dama haɗin kan na su ya lalace, kullum cikin faɗa da tashin hankali suke, sai ka ce ƙanan yara, gaba ɗaya tarbiyyar yaran sai a hankali, ba wanda yake ganin uwar wani da gashi sai tasa. Bayan tafiyar su Major, Zakiyya ta ce "Ke kin ga wani ikon Allah, wallahi saura kaɗan na haukace, na ɗauka gamo na yi, yanzu duk tsawon wannan lokacin dama jauhar 'yan biyu ne?" "Wallahi kuwa, abin da mamaki ba kaɗan ba, kuma wani ikon Allah, ba ya zancen uwar su, tun wancan lokacin" Zakiyya ta ce "Eh, amma ai yana kallon hotonta wasu lokutan, wai dan Allah maman saifu, wurin wani malamin ki ka kai Bashir, da aikin nan ya ci shi, ya manta da chubaɗo gaba ɗaya daga rayuwarsa, ashe a tagayyare haka ta haife su?" A ƙule ta ce "Ban gane wurin wani malami na kai shi ba, muka kai shi dai, ke da yarinyar nan ta rayu a gidan nan, ai da wallahi kashinmu ya bushe, yadda ya din ga rawar kan nan, ya nemi ya mayar da mu borori a kan bafulatanar daji, kawai a daina wani tone-tone" Zakiyya ta ce "Uhumm ai shikenan, zan ga yadda dramar nan za ta ƙare, shi ya ɗauki zafi shi ma wan uwarta ya ɗauka, amma abin da ya bani mamaki na kasa ganewa shi ne, yaya aka yi mijin jauhar ya samo ta, a ina ya ganota ya kawota nan ɗin?" "Oho sanin gaibu sai Allah" Su ka ci gaba da hira, su na mamakin yadda al'amuran suke cike da sarƙaƙiya da ban mamaki. *** Nabila kamar tana tura magani, haka take shan youghurt ɗin gabanta, ta na yamutsa fuska, fuskar tayi jawur, Viper ya zuba mata idanunsa ko ƙiftawa ba ya yi. "Kin ce ke youghurt, ku ma kin ƙi sha" Hawaye ya gangaro kan fuskarta ta ce "Ka takura mini ne, babu yadda zan yi, dan Allah ka nuna mini hoton 'yar uwata na sake ganinta, idan an tuna ba zan taɓa ganinta ba, wallahi sai na ji zuciyata ta buga da ƙarfi ban santa ba, amma wallahi ina son ta, meyasa tuntuni ban sanka ba ka haɗani da ita ba?" Ya shafi fuskarsa cikin dakiya ya ce "Allah ne bai ƙaddara ba" "Kenan kai nake mafarkin tana nuna mini a cikin sarƙa? Yayi ƙuri da ido yana kallon ta. "Wallahi Vi da gaske nake son ta, ashe haka ka ji, kai da ka santa ya ka ji da ka rasata, gara ma kai ni fa ban santa ba ma, tsakani da Allah iyayen nan nawa sun kyauta mini?" Tayi maganar tana rushe masa da matsanancin kuka. Allurar gefen gadonta, ya ɗauka ya buɗe ya zuƙe ta, ya ce "Kwanta ki bani hannunki na yi miki, sun shigo za su yi miki ki na salla" ta kalleshi tana sheshsheƙar kuka. "Kar ki damu, ɗan ƙwaya ne ni, kuma ɗan daba na saba riƙe sirinji da allura. Ya buɗe cannulan ya fara yi mata allurar, a hankali jikinta ya fara sanyi, ya kwantar da ita. "Tun daga lokacin da na fuskanci bijirewa ƙaddara na nufin halaka ta dindin ko samar da damejin da ba shi da hanyar gyaruwa, ya sanya na yi saranda, na bawa ƙaddarar damar ci gaba da jujjuya akalar rayuwarmu, domin na fuskanci ƙaddarorinmu na da alaƙa da juna. Tamkar na kashe kaina, haka na ji bayan rasa matata, ni har hauka na yi ai, na kuma yi ƙoƙarin sake sabauta rayuwata. Kar ki tafka irin kuskuren da na yi, nake ta fama da dana sanin da ba shi da wani amfani a gare ni,  ina guje miki aikata haka. Ki yi haƙuri ki rungumi ƙaddara, ki karɓi mahaifinki kuma ki karɓi mariƙinki, ki sasanta tsakaninsu" cikin muryar jin bacci ta ce "Maza wasu ba su yi ba, Allah sarki babarmu 'yar fulanin riga, abin tausayi" "Idan kuma abin da ya same ta ya na da alaƙa da jinsinta fa, su suka aikata komai, mu daina zargin jinsinmu da cutar da ɗaya, kawai mu mu zama adalai a kowane lokaci, da mahaifinki da major duk ba na yarwa. Zan iya rantse miki ban san mahaifinku da wani mugun hali ba, mutumin kirki ne, duk da ba ni hali na kirki, amma auren 'yar sa da na yi, ɗa ya ɗauke ni ba siriki ba" Ta buɗe idanunta da kyar, cikin raɗa ta ce "Spy, wai nasiha ka ke yi mini? To ka fara yi wa kanka, zan iya rantse maka, Abbu mutumin kirki ne, bamu haɗu a zahiri ba, a waya muka yi magana amma dattijon arziki ne" ta yi maganar daidai lokacin da bacci yayi awon gaba da ita. Dare ya fara yi, Viper ya fito daga sashin in da ɗakin Nabila yake, daga major har Baba duk suna nanz har a lokacin ba su tafi ba. Viper ya ce "Ina ganin zaku iya tafiya gida, zuwa in Allah ya kaimu da safe, tun da an ce ƙwaƙwalwarta na buƙatar hutu, kar ta rikice gaba ɗaya. Amma dai yakamata ku sasanta kanku kafin Allah ya sanya ta sake farfaɗowa". Major ya kalli Viper rai a ɓace ya ce "Ai kai ne kanwa uwar gamin komai, dan me zaka ɗauke ta, ka kai ta wurin wannan mutumin mara tsoron Allah, ita ma ya bari rayuwarta ta wulaƙanta kamar yadda ya wulakanta ta uwatta, kuma saboda rashin tsoron Allah ya aura maka yarinyar da ba ta ji ba, ba ta gani ba ka kasheta, kuma saboda zalunci ka dawo ka sanya ta tssya maka, take baka kariya, alhalin ka kashe yar uwatta, wane irin abu ne wannan?. Duk a dalilinka zumuncin da yake tsakanin yaran nan, ka watsa shi, ba ta jin maganar kowa sai ta ka, idan abin gaskiya ne, meyasa ni ba ka je ka same ni a gida, ka yi mini bayani ba kawai ka ɗauke ta ka kai wa wannan mutumin" Maganganun Major sun yi wa Viper zafi sosai, yayi ƙuri da ido yana kallon major, amma bai yi magana ba. Baba cikin mamaki ya kalli major ya ce "Ka ga wani iko na Ubangiji da yadda yake jujjuya al'amura yadda ya so, duk guje-gujen naka, da Allah ya ƙaddara, Nabila ce za ta tsaya wa mijin 'yar uwatta, ka yi ƙoƙarin tsayawa a kan iliminta da tarbiyyarta, amma Al'amin ba mutumin banza ba ne ba, haryanzu ban yadda zai iya kashe mini 'ya ba, kar ka ƙara danganta shi da kisan kan jauhar" Saifu ya ce "Baba ka daina wannan maganar fa, ba ka da tabbas ya aikata ko be aikata ba" Liti ya ce "Ji wani ɗan wahala kuma, to ai sai ka jira kotu ta tabattar da shi ya aikata, tun da shari'a za a fara kwanan nan. Mu mu ka yi rayuwa a gidan Viper a tsakanin sa da Jauhar. Mun san yanayin zamantakewar su, tsabar ƙauna ko sunanta ba ya iya faɗa sai 'yar madara, sai ka jira kotu tukuna, kafin ka yi wannan maganar" Shiru saifu yayi, dan ya san halin liti farin sani, 'yan a mutun mai zamani ne. Da kyar da siɗin goshi, aka samu suka tafi gida, shi ma sai da su ka tabbatar da Nabila tana cikin tsaron da babu wanda zai gudu da ita, dan kowa zargin kowa yake yi. Viper a makwancinsa, yana ta jujjuya al'amarin ya san akwai sauran ƙura a gaba, major ya ɗauki zafi sosai da sosai, kuma haɗin kansu ne zai ba wa Nabila nutsuwar ci gaba da gudanar da shari'ar da take yi a cikin nutsuwa. *** Sumayya duk wani abu da ya shafi Indabo, haka take yaɗa shi a kafafen watsa labarai ba tare da tsoro ko fargaba ba, ba shi kaɗai ba, mussaman Alhaji mu'azzam yake sanyawa ake nemo mata manyan rahotanni na bankaɗa tare da cikakkiyar hujja a kan miyagun harƙallolin da ake yi a ƙasar nan. Sai dai kash, ko an bankaɗo babu wani abu da talaka zai iya yi a kai face Allah ya isa. Dan ƴan siyasar sun din ga ƙoƙarin kare kansu kenan, lokutan zaɓe su sake lallaɓowa tare da fara ayyukan babu gaira babu dalili, da raba tallafin abin da bai kai kaso goma a cikin abin da suke wawaso na al'aumma ba. Sai dai a wannan karon al'ummar sun yi rawar gani wurin yin abin da ya dace, karo na farko a Nigeria da ake ƙoƙarin yi wa sanata kiranye. Duk da irin barazana da matasan da suke jagorantar abin suke yi, amma suka dage babu gudu babu ja da baya, dan tuni sun miƙa wasiƙa ga hukumar zaɓe ta ƙasa a kan son yi wa Indabo kiranye. Hakan ya ba wa wasu matasan daga sassa daban-daban na ƙasar nan ƙwarin gwiwa da ganin cewa ashe za su iya kawo canji ga waɗanda suke wakiltar su su ma. Alhaji mu'azzam mutum ne na mutane, dan haka mutanensa su ka din ga kiransa a kan ya fito takara. Dama harin kujerar inda Bayan kammala program ɗin ta, ta ga kiran waya. Lambar Nabila ta gani, ta ɗaga ta ce "Ke ya ne, program na kammala ko numfashi ban shaƙa ba, kin doko mini kira" "Ta na asibitin barrack, ta na buƙatar ganinki da gaggawa" ƙuuu cikin sumayya ya yi ƙara, muryar Viper ce, a duniya Allah ya yi masa kwarjini, muryarsa da ta ji kawai gabanta ya faɗi. Kashe wayar ya yi, bayan kammala gaya mata saƙon. A gurguje Sumayya take ƙoƙarin kammala ayyukanta, dan ya je ya ji me ya sami Nabila. A jiya da major ya koma gida, kasa gane kansa matansa suka yi, dan babu wadda ya kula, kuma ya ce baya buƙatar kowa ta zo masa turaka. Sai Nasir suka tutsiye, su na tambayar sa, ina su ka je jiya wuni guda ba sa nan. Nasir ya labarta musu komai, gaba ɗaya suka yi shock. Anty ta ce "Dama mahaifin Nabila yana raye?" "Eh, mun ganshi jiya ma, ɗan daban nan Viper da ake nema, 'yar biyun Nabila ya aura ya kashe, kuma saboda shirme take kare shi, shi ya ɗauke ta ya kaita wurin mahaifinta" al'amarin yana buƙatar nutsuwa kan a warware shi, dan ba kowa ne zai iya fahimtar bayanin ba sama-sama. Ko da sumayya ta je, ba wanda ya hanata shiga, da ta tambayi in da Nabila take, Nabila na ganinta ta miƙe tsaye, fuskarta ta kumbura suntum saboda kuka. Ta rungume sumayya ta ci gaba da kuka, Sumayya ta ce "Subhanallah, Nabila waye ya mutu? Kin ga yadda ki ka rame fuskarki ta kumbura kuwa?" Cikin kuka ta ce "Sumayya na ga babana jiya" waro ido sumayyan tayi ta ce "A ina?" "Viper ne ya kai ni, Sumayya ashe yar biyuna ya aura aka kashe, duk wannan haƙilon da nake yi, 'yar uwata aka kashe" Sumayya ta ƙurawa Nabila ido, ta ce "Anya kanki ɗaya?" "Kai na ɗaya Sumayya, amma ai kin san lokacin da nake ce miki ina mafarki da mai kama da ni, ki ke yi mini dariya, wallahi sumayya ina da 'yar uwa da ban taɓa ganinta ba, a kanta nake shari'ar Viper" "Nabila, gaba ɗaya kin rikita ni, ban gane in da ki ka dosa ba wallahi, gaba ɗaya na rikice" Viper ne ya turo ƙofar ɗakin ya shigo. Jiki na rawa sumayya ta gaishe shi ya amsa, ta kalli Viper ta ce "Vi ka yi wa sumayya bayani, ta ƙi yadda ta kuma kasa gane bayanin da na yi mata" "Wa zai fuskanci wannan bayanin naki at once dama, ki ƙwarara jikinki, ki yi haƙuri ki daina wannan kukan, yana daga dalilin da ya sanya tun farko ban gaya miki ba" Sumayya za ta yi magana, Abba ya turo ƙofa ya shigo da sallama, suka amsa masa. Sumayya ta gaida Abba ya amsa mata, suka gaisa da Nasir ma. Viper ya yi masa barka da zuwa, amma ya yi masa shiru. "Arfa, kin ji sauƙi ina son a sallame ki, mu koma gida ne" kawar da kanta gefe ta yi, ba ta kalle shi ba. Sumayya ta ce "Nabila Abba ne fa" Ta ɗaga kai ta kalli Sumayya ta ce "Abba disappointed me, meyasa ya ɓoye mini ina da 'yar uwa, gashi ta mutu ban taɓa ganinta ba... "Wai mahaifiyarki ma ba rasuwa ta yi baki taɓa ganinta ba?" Viper ya yi maganar a kausashe. "Amma jauhar ta yi tsawon rai ai, meyasa aka hukunta mu da laifin babanmu" Nasir ya ce "Nabila Abban ki ke gaya wa haka?" Major ya yi shiru, kawai ya tashi ya fita. Sumayya ta ce "Nabila meyasa ki ka yi haka? Baki kyauta ba, duk ɗawainiyar da ya yi da mu, hakan da ki ka yi ba dai-dai ba ne ba. Idan aka sallame ki, dole mu je ki ba shi haƙuri. Kiran gaggawa aka yi wa sumayya, ta tashi ta tafi, cike da mamaki da tunani daban-daban a cikin zuciyarta. Bayan tafiyar major, sai ga Bashir, har da kayan abinci niƙi-niƙi sun zo duba Nabila. Tana zaune, a kan gado, Viper yana gefe yana waya, yana ganinsu ya kashe wayar, ya risuna suka gaisa da Baba. Ƙarasawa yayi gaban gadon Nabila ya zauna ya ce "Sannu ya jikin naki?" Ƙura masa ido ta yi, amma ta kasa masa uffan. Ya zauna ya dafa hannunta, amma ta janye ta sunkuyar da kai. Bashir jiki a sanyaye ya tsaya yana ci gaba da kallon Nabila. Viper ya ce "Ina ga ko zaka ɗan bata lokaci, kafin Nabila ta ganka, tana ɗokin da muradin ganinka, abin da ta ji ne dole za ta ji wani iri, amma in sha Allah za ta maye maka gurbin jauhar. "Na san ni mai laifi ne, amma ƙaddara ta riga fata, wallahi tamkar an shafe ni tunanina a cikin kaina, haka na manta da mairamu. Yaya za ayi ace ka auri mace ka manta da ita, ban san meyafaru ba a lokacin. Kuma ni maitama bai gaya mini ku biyu ba ne, amma ki yi haƙuri ki yafe mini dan Allah" ya kalli Viper ya ce "Bari na je, hafsa ma za su zo dubata yanzun nan in sha Allah" Viper ya tashi ya raka shi har harabar Asibitin. Nabila ta jingina da jikin bango ta lumshe idanunta, hawaye na bin gefen idonta, Viper ya dawo ya tarar da ita. "Ba ki kyauta ba abin da ki ka yi? Duk ɗokin ganin mahaifin naki, abin da ki ka yi kin kyauta kenan?" "Ba ka san me nake ji ba ne?" "Ko ma me ki ke ji ba ki kai ni ba, abin da ki ke yi ba ki kyauta ba, ke zaki jajirce ki daidaita wannan rashin jituwar da yake tsakaninsu, ki rungumi mahaifinki" Ta zuba masa ido hawaye na bin idonta. "Menene kuma? Kukan be isa ba haka?" "Vi" tayi maganar muryarta na rawa. "Abla" "Ka ga abin ƙaddara ko? Ƙaddara ce ta sanya na din ga bibiyarka" Ya ce "Haka ne" "Kwatsam na fara sonka daga wasa, na yarda da maganarka, ba zan taɓa jauhar ba, kuma idan na ci gaba da sonka ban yi zumunci ba na ci amanar 'yar uwata. Zan fara jin kunyrka a matsayin ka na mijin yayata, ba soyayya tsakanin mu yanzu, zan yi iya ƙoƙarina na ga an ƙwatarwa 'yar uwata hakkinta, kuma na ga an wanke ka daga zargin da ake yi maka. Na gode sosai da sosai da ƙoƙarin da ka yi mini". Ayshercool 08081012143 88 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Abin da Nabila ta faɗa ya sanya Viper jin ƙirjinsa ya tsananta bugawa. Ta sake cewa "mu yi zumunci kawai, zumuncinmu ya ɗore, amma yanzu na fahimce ka, da ka yi ta jaddada mini, ba zan taɓa zamo wa jauhar ba" zai yi magana. Hafsa ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo da sallama, hannunta riƙe da leda cike da kayan marmari, ta ƙarasa tana murmushi. Bayanta saifu ne yake biye da ita, tana zuwa ta dungurar da ledar ta zauna a kusa da Nabila ta ce "Waliyiyya kin warke ya jikin?" Nabila ta yi murmushi, ta fuskanci Hafsa 'yar uwatta ce, dan tana kama da ita kaɗan, ta ce "Jiki Alhamdilillah". Ta kalli Viper ta risuna ta ce "Ina wuni" "Lafiya ƙalau yaya hafsa" ya kirata da yadda jauhar take kiranta. Sai ta yi murmushi ta sake kallon Nabila ta ɗora hannunta a goshin Nabila ta ce "Ba kya zazzaɓi ma, kin warke sai mu tafi da ke gida ko? Ko gidanku zaki koma ke da shi? Har gidan naku nake zuwa ba a sani ba, baba ya ce idan na kuma zuwa Yaya tijjani ya zane ni" Saifu ya kalli Nabila ya ce "Yaya jikin naki?" Nabila ta ce "Na ji sauƙi Alhamdilillah" "Allah ya sauwwaƙe, ga hafsa nan ita ma yar uwammu ce, yakamata ace duk an gabatar miki da yan uwanki, amma sai Allah ya sa kin warware, zan je duba wani abokina, idan na dawo zan zo na ɗauke ta. Ina amfani da wannan damar wurin baki haƙuri, da nema wa mahaifinmu afuwarki ki yi haƙuri dan Allah. Sannan ku yi haƙuri da abubuwan da za ta yi, tana misbehaving wasu lokutan, tana fama da matsalar ƙwaƙwalwa ne, ta damu a kawota wurin ki ne" "Baba ya ce kar ka sake ce mini mahaukaciya, ni da hankalina dan Allah jauhar na yi kama da mahaukaciya?" Hafsa tayi maganar kamar zata yi kuka. Nabila ta girgiza kai ta ce "Ko kaɗan" Saifu ya juya ya tafi, ba tare da wani ya kula wani tsakanin sa da Viper ba. Bayan ya fita Hafsa ta ce "Jauhar ina jaririnki ne?" Viper ya ce "Ba jauhar ba ce ba" ta kalli Nabila ta kalle shi ta ce "Ita ce mana" Ya ce "Kalle ta da kyau dai" ta sake ƙurawa Nabila ido, ta kalleshi ta ce "Jauhar ce mana, ina ɗan naku to?" Ya ce "Tambayeta" Nabila ta ce "Ta tambaye ka dai" Viper a hankali ya ce "Ya rasu" Ta ɗan yi shiru ta ce "Shi ba zai dawo ba kenan kamar yadda ita ta dawo, to yaushe zata samu wani cikin, ina son na ga ta haihu wallahi, ka san baba cewa yake yi, idan ku yi aure ku haihu da ƙuruciyarku, sai su zama kamar ƙannenku" gum Nabila tayi jin katoɓarar da Hafsan tayi. Gaba ɗaya suka yi mata shiru, ta kalli Nabila ta kalli Viper ta ce "Baku gaya mini ba" Viper ya kalli Nabila ya ce "Abla tana magana, yaushe zaki sake samun wani cikin ki haihu?" Nabila ta ce "Na shiga uku"ta yi maganar tana sunkuyar da kai, sai ya faɗi magana ya wani maze kamar ba shi baz wannan nannauyar maganar tayi masa sauƙin faɗa haka yana kallonta. Ya basar ya ce "Ina mijinki ne?" "Ni bani da aure, rabuwa muka yi, uwargidansa ta hana shi kula ni, sai dai ya ɗauketa su tafi yawo su bar ni a gida. Nayi ta kuka na gaya wa Anty, amma wai na yi haƙuri, na zo na daina bacci, na je asibiti aka bani wani magani na kwana biyu, tun daga ranar da nayi bacci na ji daɗi, na din ga kai wa wani mai chemist yana bani ina sha, har ya fara ƙara mini da wasu ina sha. Gaba ɗaya baya yi mini irin yadda ka ke yi wa jauhar, idan na zo gidanku naga yadda ku ke yi, in yi ta kuka, kuma fa anty ce ta din ga bani magani dan ya aure ni, amma wallahi ina son shi, na din ga shaye-shaye da ban san shi nake yi ba sai daga baya. Zama yaƙi daɗi ya sake ni. Bayan ya sake ni fa sai da ya auri wata kuma ta zauna ita ba ayi mata irin yadda aka yi mini ba. Na cigaba da shaye-shaye damuwa ta yi mini yawa, mai chemist yayi mini haɗin wata ƙwaya ya ce zan manta da damuwata ashe ƙwaƙwalwa ta ya taɓa mini sai aka ce wai na zama mahaukaciya. Amma nima na san alhakin ki ne ya kama ni, ki yafe mini dan Allah ƙanwata" Nabila da tausayin Hafsa ya sanya ta fara hawaye, ta kalle ta ta ce Jauhar zuciyarta daban ce, ta musamman ce. Ita ai kusan kun gama yi mata komai da ku ka aura mata sanyin idaniyarta. Turo ƙofar ɗakin aka yi hafsa ba ta waiwaya ba, amma ta tsorata gabanta ya faɗi, jin ƙamshin turaren Alhaji mu'azzam ya cika ɗakin. Sallama ya yi suka amsa masa, ta ɗaga kai a hankali, suka yi ido huɗu da shi, gabanta ya sake faɗuwa, zai iya cewa tun da ya saketa bai sake ganinta ba sai yanzu. Jan jikinta tayi, ta haye gadon da Nabila take. Ya miƙa wa Viper hannu, amma Viper ya tsaya yana kallon sa, Nabila ce ta ɗan gyaɗa masa kai, a hankali ya miƙa masa hannu, suka yi musabaha. Ya ja wata kujerar ya zauna. Ya ce "Barrister ya jikin?" "Alhamdilillah" ta amsa a hankali. Ya kalli Viper ya ce "Ashe ka kawo ƙarshen labarin da kanka?" Viper fuskarsa babu yabo ba fallasa ya ce "Eh na kawo" "Na san kan labarin ya ƙarƙare da sauran rina a kaba, ina yi muku fatan alkhairi. Nabila zuwa yanzu kin san wanene ni, da dalilin da ya sanya na din ga bibiyarki, ta tabbata jauhar Sister ɗinki ce ko? Duk na san mahaifinki, ban yi garajen sanar da shi komai ba, saboda binciken da nayi a kanki, babu ta in da ya nuna jauhar da ke akwai alaƙa, ashe akwai ɗin dai. Na tayaki murna" Nabila ta jinjina kai ta ce "Na gode sosai, Jauhar da ni twins ne, abubuwan ne da tsayi sosai amma bani da bakin yi maka godiya Allah ya saka da alkhairi. Ga wannan ita ma tana cikin 'yan uwana, sunanta hafsa" Ya kalli hafsa da tayi tsuru, yayi murmushi ya ce "Na santa ai, hafsa mun san juna ko?" Hafsa ta kalleshi, kawai ta dira ta ɗaya side ɗin, ta zari takalmanta za ta fita, Nabila ta ce "Ina zaki je?" Ba ta juyo ba ta ce "Waje zafi nake ji, kar ki da mu ina da hankali ba wani wurin zan je ba" ta kai bakin ƙofa walid ya turo ƙofa ya buge mata goshi. A rikice ya ce "Ya salam, yi haƙuri dan Allah, ban dan kin taho ba" ta yi murmushi ya ce "Bakomai ai babu zafi tayi waje. Suka shigo ɗakin, suka gaisa da Alhaji mu'zzam, ya tashi da hanzari ya ce "Bari na je waje na amsa waya, daga nan zan wuce, amma ina son zama da ku, a kan shari'ar nan amma ina zuwa dai" Alhaji mu'azzam ya fice daga ɗakin. Kawai suka ga Viper ya saka dariya, gaba ɗaya suka zuba masa ido, Nabila tunani take yi, anya ta taɓa ganin dariyar Viper haka. Walid ya ce "Mutumina meyafaru ne ka ke dariya, dariyar da rabonka da ita tun 'yar madara na raye" Ya ce "Muhsin, wani abu ne ya bani dariya" "Akhbirni mutumina, meyafaru ne?" Ya tsagaita ya mayar da dariyar murmushi ya ce "So mugun wasa ne, mai saka ma'abocinsa yi masa biyayyar dole ko bai shirya ba, babu wata waya fa da zai amsa, ya bi matarsa ne kawai, maybe yana kewarta" Nabila ta ce "Ita ce Hafsan da oga walid ya bani labari, dama zancen Alhaji mu'azzam take yi?" Viper ya jinjina mata kai alamar eh. "Ikon Allah, yanzu duk tsawon wannan lokacin kun san komai, ku ka rufe ni" Viper ya ce "Yanzu ai gashi kin sani". Can bayan ɗakin Nabila ta zagaya, hawaye na zubowa daga idanunta, ta tsaya tana ta share hawayenta, ta jima a tsaye tana share hawayen, sannan ta juyo da niyyar komawa, kawai ta ga Alhaji mu'azzam a bayanta a tsaye. Tsuru-tsuru ta yi kamar mara gaskiya. "Haba hafsa, ko gaisuwa babu, tamkar dodo daga ganina sai ki hau gudu? Ya goshin naki?" Cikin inda inda ta ce "Lafiya ƙalau, babu zafi" Alhaji mu'azzam ya ce "Ya kumbura fa, kuma ki ce babu zafi?" Ta ɗaga kai alamar eh. Ya taka a hankali zuwa gabanta, ya mamaye ta da ƙamshin turaren sa, ta kalleshi, yana sanye da yadi ash mai tsada riga da wando, Alhaji mu'azzam akwai kwalliya da ado. "Kin ga wata sabuwa daban mai kama da jauhar ko?" Ta girgiza kai ta ce "A'a jauhar ce". "Ba jauhar ba ce, wannan sunanta Nabila. Hafsat" ya kira sunanta a hankali. Tsigar jikinta ta tashi, taƙi kallonsa. "Meyake damunki ne? Kin rame kin yi duhu, ba gayunki kamar da, meyafaru haka?" Kawai kuka ya ƙwace mata, har da sheshsheƙa. Jauhar yake so ba hafsa ba, amma yana tausayin ta mussaman da ya ganta yanzu. Daga baya ya fuskanci ba wai kuɗinsa kawai take yi wa ba, tana matuƙar son sa. Amma shi kansa bai san ya aka yi ya din ga misbehaving ba, kuma a lokacin ƙanwar indabo tsohuwar budurwarsa jidda tana ta bibiyarsa ya aureta. Handkerchief ɗin sa ya ɗaukko, ya fara share mata hawayen. Ƙoƙarin rasa nutsuwar sa ya fara yi, ita ma ganin idan ta cigaba da tsayuwa, za su iya ɓarna, dan har wani tsuma take yi, soyayyar sa ƙamshin turaren sa, da maganganun da ya fara yi mata, narka mata zuciya yake yi, hakan ya sanya ta buge hannunsa daga fuskarta, ta raɓa shi ta bar wurin. *** Abdul yana kwance a gadon asibiti, hannunsa ɗaya da ankwa, mahaifiyarsa na gefe tana ta uban kuka, tamkar an ce mata gawar Abdul ce a gabanta. Ga Indabo can yana fuskantar hukunci. Jami'an tsaro na son ɗaukar statement dan a shiga kotu, amma ko magana ba ya iya yi, idan ya yinƙura sai aman jini. Bunkure ma kamar zata haukace, dan ko ta wani ɓangare tana samun suka, kuma babu sassauci. Mutane sun fara juya mata baya, tare da gazgata zancen Nabila da tayi a kanta a kwankin baya aka din ga attacking ɗin ta. Nabila ta bar Asibiti, ta koma gidan madam Halima. Viper ya dage da yi wa Nabila nasiha, tare da tausarta, a kan ta karɓi mahaifinta, tayi haƙuri sannan ta nemi gafarar major shi ma, dan bai cancanci abin da tayi masa ba. "Ni ka ƙyale ni dan Allah, in ji da raɗaɗin rashin 'yar uwata da hake addabar ruhi da gangangar jikina, koma menene ya faru laifinsu ne na kasa samun nutsuwar karɓar dukkaninsu". A fausace ya hau ta da faɗa "Are you out of your sense, rayuwata ba ta zama darasi a gare ki ba? Duk abin da ya faru a tsakaninsu, ke ina ruwanki ne a ciki? Could you imagine mahaifinki na yi mini kuka a kan na shawo masa kanki ko sau ɗaya ki yi masa kallon uba, ya riƙe ko da hannunki ne, ya ji daɗi? Ya rasa jauhar, babu tsammani kin bayyana a gare shi, ba tare da ya san ki na raye ba, amma kin ƙi saurarsa ina ruwanki da abin da ya riga ya wuce? Wallahi ko kaffara ba zan yi ba da yar uwakki ce ba zata yi haka ba, jauhar ta daban ce, mai tausayi da jin ƙai ce. Na san da ke aka yi wa abin da aka yi mata a kaina bijirewa zaki yi. Da haƙuri da siyasa ake cin ribar zaman duniya ba fushi da shirme ba. Kin nuna rashin jin dadin ki abin da aka yi miki da farko daga baya kuma sai ki saukko ki haƙura ai" Sumayya da tana wurin, ita kanta sai da ta tsorata da faɗan da Viper yake yi. Nabila kuwa kuka take yi wiwi, wasu lokutan gara faɗan Abba da na Viper, gaba ɗaya sai ya razanata ya saka ta rasa abin da yake yi mata daɗi. "Ki tashi ki shirya, zamu je ki nemi afuwarsa, sannan mu je mu ga ɗan mama, da su Rahama" Haka Nabila ta shirya, sumayya tana ta mamakin samun abin da zai iya tsorata Nabila ya sakata kuka, bayan Abba. Yau ma a ƙofar gidan su jauhar, aka yi parking, tare da sumayya suka zo, da sallama suka shiga. Baba yana gareji, yana ba wa saifu sallahun wanke masa mota, Nabila suka shiga. Cak ya tsaya yana kallon su, da sumayya da Nabila. Kallo ɗaya Sumayya ta yi wa Baba ta gane baban Nabila ne. Rikicewa yayi ya nufota duk da jikinsa a sanyaye ya nufeta, idanunsa cike da hawaye. Yana ƙarasowa ta faɗa jikinsa tana sakin wani irin kuka mai karya zuciya. A hankali ta ce "Baba" tana kuka yana kuka, kamar wani zai ƙwace masa ita, haka ya ƙanƙame Nabila, yana kuka har da majina. Sumayya da take tsaye ita ma fashewa ta yi da kukan, cikin matsanancin tausayin su, ta san irin artabu da ƙalubalen da Nabila ta din ga fuskanta a kan rashin uba, a gidan major yadda suke kiranta da tsintacciyar mage wai babu wanda ya san babanta, Nabila ba ta da wata magana da ta wuce fatan ganin mahaifinta, ta ji ina ma ita ma tana da rabon sake ganin mahaifinta a rayuwa. Viper yana hango su daga waje, ya sunkuyar da kansa hawaye na cika masa ido, cike da fatan ina ma shi ne ya sake ganin Jauhar ta bayyana a rayuwarsa ba tare da ya yi tsammanin hakan ba. Nabila ta ce "Sumayya ga babana, kin ga babana" "Na gan shi Nabilata, Ina tayamu murnar ganin Baba, burin da muka daɗe muna fatan Allah ya cika mana" "Ki yafe mini 'ya ta, abin da ya faru ba da son raina ba ne ba, wani abu ne da ba zan ce ga a yadda ya faru ba, na san mai laifi ne a gareku da mahaifiyarku, ke kaɗai ki ka rage mini a cikin su, dan Allah ki yi haƙuri ki yafe mini" yayi maganar cikin matsanancin kuka. Ya rungumi Nabila zuwa cikin gidan, sumayya na biye da su, yaran gidan duk su ka kewaye su, wasu na taya su kuka wasu na kallon su. Ya ce aje a ce wa Al'amin ya shiga. Nabila ta kwantar da kanta a kan cinyar baba, tana cigaba da kuka. Bayan Viper ya shigo su ka gaisa da Baba, ya kalli sumayya ya kalli Viper ya ce "Anya Aminullahi wannan ma ba tawa ba ce?" Viper ya yi murmushi ya ce "Duk naka ne Baba, an baka" "Na san fuskarta ne, ta na kama da wani wanda na sani, amma ba zan iya tuna waye ba? Ya sunan mahaifinki?" Sumayya ta share hawayenta ta ce ba ni da wayon sanin mahaifina, amma dai sunansa Tahir ladan. A take ya yi sak, ya ce "Wane Tahir ladan ɗin? Coustom ne?" Sumayya ta jinjina masa kai ta ce "Ka san shi?" Yayi shiru ya ce "Tare mu ka je ɗaurin aurena a jalingo, abokin aikina ne, lokacin da aka yi mini transfer daga in da na bar mairamu shi ne ya koma, ya je yayi reporting a wurin aiki, ya koma yayi hatsarin mota ya rasu. Viper ya ce "Kenan dai duk 'ya'yan naka na kawo maka" Kamar ƙaramin yaro ya kalli Sumayya ya ce "Ni babanki ne, ke ma 'ya ta ce ai, na gode Aminullahi, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi" Viper ya ce "Baba da ka yi haƙuri da kukan nan haka, saboda su ma su samu ƙwarin gwiwar yin haƙuri, mu gode wa Allah kawai" Ya jinjina kai yana maimaita Alhamdilillah. Baba ya din ga shafa kan Nabila, amma hawayensa suka kasa tsayawa. Zakiyya tare da maman hafsa su ka shigo ɗakin da sallama, su na kallon yadda ya saka su Nabila a gaba yana kuka. Viper ya na ganin Zakiyya ya haɗe rai, tamkar ya ga abin ƙyama. Su ka zauna su ka din ga surutai marasa ma'ana, marasa tushe balle makama. Tare da taya su kukan cike da makirci. "Baba ina hafsa?" Nabila ta tambaya da kyar. "Ta je gidan kakaninta da su ka haifi mahaifiyarta". "Baba shikenan ban san jauhar ba, ba kuma zan ganta ba, ban san mama ba, ita ma kuma ban santa ba, mun rayu a wurare daban-daban, ba mu san juna ba" tayi maganar tana sake fashewa da kuka. Cikin sigar rarrashi ya ce "Hakan hukuncin Allah ne, ki yi haƙuri, mu masu tarin laifi ne a wurinki, mussaman ni, na san ni ne baban mai laifi, duk da major ma mai laifi ne, bai kamata ƙiyayyar da yake yi mini ya sanya, ya nesanta ni da ke ba, ya kawo mini yarinya amma bai kuma waiwaiyarta ba, amma Alhamdilillah na ji dadin yadda ya kula mini da ke" Viper ya numfasa ya ce "Baba yakamata mu koma haka, da su" Baba ya ce "Aminullahi, dan girman Allah ka bar mini ita" "Ka yi haƙuri, ai aikin gama ya riga ya gama, tun da har komai ya riga ya bayyana, sai da na saka hannu na ɗauki excuse sannan na fito da ita, shi ma bisa uzurin aiki za ta yi, kuma ka ga a hannun Abba aka yi yarjejeniya a ka ɗauketa, da niyyar ba ta kariya, har a kammala shari'ata, addu'ar ka muke fata". "Yanzu ka na nufin mijin 'yar uwatta take karewa, Allah al-hakimu, Allah ya bayar da nasara, yayi muku jagora dukkaninku" Su ka amsa da Amin gaba ɗaya. Baba ya ce ya bari su ci abinci, Viper ya ce "Lokacinsu a ƙididdige yake, idan su ka saɓa akwai matsala" Har gaban mota ya rako su, yana rungume da Nabila kamar zai mayar da ita cikin sa. Su ka je bakin motar, ya riƙe hannun sumayya, ya riƙe na Nabila, ya kasa tsayar da hawayensa, ya kalle su ya sake fashewa da kuka ya ce "Ku yafe mini dan Allah, ku ci gaba da haɗa kanku, Allah ya yi muku albarka, Allah ya jiƙan mahaifinki ke kuma Allah ya jiƙan mahaifiyarki da jauhar" Su na kuka su ka shiga motar, su ka ja, su na tafe a hanya, Viper bai rarrashe su ba, dan ba wani ƙwarewa ya yi a hakan ba, ya yi musu shiru, su ka yi ta kukan, ya ce a fara kai sumayya gida, sannan su koma barrack washegari sai su je wurin su ramma. *** Major ya sha mamakin yadda Nabila ta nuna fushi take yi da shi, taƙi saurarsa. Mama kuwa sai ziga shi take yi, ta ce "Dama ga ubanta yaushe za ta saurare ka, ai kai ka gama yi mata amfani kuma, shiyasa tuntuni da yaranka ka kama, da ya fiye maka" shi dai bai furta komai ba, amma abin ya din ga cin zuciyarsa. Rahila ma aka sallameta daga asibiti, bayan an yi mata ɗorin karayar hannunta, sai da Abbu ya dage ya ce sai Abba ya bar masa gidansa, aka kaɗa aka raya ya ce ba zai ci gaba da riƙe shi ba, idan kuma ta dage sai ya zauna, to sai dai ta bi shi su bar gidan. Shahida ma ta dage a kan raba aurenta, da fari Abbu bai sani ba, amma bayan ya takurata, da ta gaya masa bai tausayawa halin da rahila take ciki ba, yayi mata tas, ya ce sai an raba auren, ba za a saka masa 'ya a halaka ba. *** Sumayya ta labartawa ummanta abin da yake faruwa, sumayya na ce mata jalingo, ummanta ta ce ta san mahaifin Nabila, amma ba wani sani ba, ta dai san abokin aikinsa ne. Madam halima ta gaya wa Nabila Viper ya zo, yana jiranta su fita. Kallo ɗaya ya yi mata, ya san ba ta samu isasshen bacci ba, fuskar nan babu walwala. "Ina kwana" tayi maganar a hankali. Ya tsura mata ido, ita kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa. "Akwai sauran damuwa ne? Kin haɗu da mahaifinki ba shi ne fatanki ba?" Yayi maganar yana kallon ta. Ta girgiza masa kai. Ya ce "To me ya yi saura kuma?" "Kewar yar uwata, da tunanin yadda zan daidaita Baba da Abba, kowanne ya na da muhimmanci a gare ni, amma Abba ba zai saurare ni ba, saboda Nasir ba zai daina ziga shi ba, saboda haushin tsaya maka da na yi, zai ta ziga shi a kan lallai ya yadda kai ka kashe jauhar, ba ni da gaskiya ina tsaya maka" "Ƙalubale ne ma hakan, amma yakamata tun ba yanzu ba ki san kuka ba magani bane ba, na san duk ni ne silar komai, shigowa ta rayuwarki, ki yi haƙuri" "Ba kai ka shigo rayuwata ba, ni na shiga taka, ko in ce ƙaddara ce, amma in sha Allah zan yi iya yi na, sai an hukunta wanda su ka kashe 'yar uwata, ku ma na tabattar da an kwance sarƙar da aka sanya wa mijinta alƙawari ne na yi wa kaina" ta yi maganar tana share hawayenta. Ya jinjina kai ya ce "Allah ya ba da sa'a" "Amin" har ya yi gaba zai fita, ta ce "Viper" ya tsaya ya waiwayo. Ta ƙarasa gabansa ta ce "Ina son ka ji abin da na ji a lokacin da na rungumi mahaifina, ina son ka yi amfani da nasihar da ka yi mini, a kan kanka. Mahaifinka yana da muhimmanci a rayuwarka" "Wannan ni ya shafa, ba ke ba, dan haka babu ruwanki a ciki" Ta ɗan yi murmushi ta ce "Ina roƙonka ne a matsayina na ƙanwarka, ba lauyar ka ba, ina fatan ka kasance cikin rahamar Allah kamar yadda nima ka ankarar da ni nawa kuskuren" Ajiyar zuciya ya yi, ya fice ta bi bayansa. Haka kurum su na tafe a mota, yake tunanin da gaske yanzu Nabila a matsayin yaya ta ɗauke shi kawai?. Harabar wurin 'yan sandan cike da motoci. A can su ka tarar da sumayya, mahaifiyar ramma ma ta je wurin ita da ramma, Alhaji mu'azzam ya saka an kai su. Nabila tana matuƙar jinjinawa gudunmuwar da Alhaji mu'zzam ya ba su, ya cancanci yabo da godiya, amma goga Viper hakan ko a jikinsa, balle ya nuna masa yabawar sa da jin daɗin sa. Suka gaggaisa, ramma da ƙyar ta iya gaida Viper, saboda matsanancin tsoronsa da take ji. Su liti tuni sun je wurin, dan sun kai wa ɗan mama abinci. Sumayya ta zauna su ka sake tattauna wa da ramma, kasancewar su na jiran ƙarasowar su Abdul da lauyoyin sa a ɗauki statement ɗin su duka. Sumayya ta naɗi wani sashi mai muhimmanci, na tattaunawar su da ramman, wanda zai yi wa Sumayya amfani haka Nabila, mussman ta ɓangaren Naja'atu Bunkure. Viper kuwa cikin isa yake yawonsa a headquarter yan sandan, ya je ganin ɗan mama da kansa. Sumayya ta dubi Nabila ta ce "Nabila, haryanzu ina mamakin yadda aka yi ki ka haɗu da Viper, ikon Allah ashe duk wannan haƙilon a kan sister ɗinki ki ke yin sa, amma Nabila idan ba shi ne ya kashe Jauhar ba, wanene?" Nabila ta gyaɗa kai ta ce "Mu haɗu a kotu kawai sumayya, abubuwan su na da girma da faɗi sosai" "Meye wani sai mun haɗu a kotu, ki ƙarasa mini, kin bar ni a cikin duhu da zullumi Abla, kamar yadda na ji ana kiran ki, Nabila gayen nan kuwa ba son ki yake yi ba?" Nabila ta numfasa ta ce "Sumayya, ba ki yi ƙarya ba, ni ina son Viper, na kamu da sonsa ba tare da na shirya hakan ba, dan da farko dan na taimaki rayuwarsa ya dawo hayyacinsa ya sanya na ce ina son sa, sai dai ban yi aune ba, na faɗa son shi da gaske. Saboda Viper mutum ne na musamman ya kai a so shi, kin san meya ƙara jefani cikin ƙaunar sa da gaske?" Sumayya ta ce "Sai kin faɗa" "Zamantakewar sa da ya yi da jauhar" Nan Nabila ta fara ba wa sumayya labarin abin da ba ta sani ba, matakan da ta bi wurin haɗuwa da shi, zuwa labarin sa da Walid ya bata. Ramma ta yi shiru ta na sauraron su, kawai ta din ga jin, idan jauhar tayi haƙuri da Viper mutum mai ban tsoro ta zauna da shi, ta yi wannan gwagwarmayar lallai idan aka yi haƙuri Abdul ma zai iya shiryuwa. Wani ɗan sanda ne ya leƙo, ya ce su shiga, sun ƙaraso. Gaban ramma ya faɗi, maman ramma na can ta na shan hantsi, Nabila ta yi mata magana ta ce ta taso. Gaban ramma ya tsananta faɗuwa, aka yi musu jagora zuwa ofishin da za a ɗauki statement ɗin. A ciki su ka tarar da Viper a zaune, har da manyan mutane abokan Indabo da su ka zo, ga mahaifiyar Abdul yasar a wurin ita ma. Ai su na shiga office ɗin, Abdul ya miƙe, kallonsa ramma ta yi, ya rame sosai da sosai, ba wai rama ta damuwa ba, rama ta ciwo. "Rahama" ya kira sunanta a raunane. Mugun kallon da Viper ya yi mata ne,ya sanya ba shiri ta nemi wuri ta zauna. Tashi ya yi ya nufi in da take, wani ɗan sanda ya daka masa tsawa, amma bai saurare shi, ba ya nufi ramma. Ƙafa Viper ya saka masa, abin ka da mara lafiya, ya tafi luu zai faɗi, Viper ya riƙe rigarsa ya hana shi kai wa ƙasa. Aka saka ɗan sanda ya janyo shi, ya zaunar da shi, tuni ramma ta fara kuka. Kawai ya zuba mata ido ko ƙiftawa ba ya yi. "Abdul da ma wannan ce yarinyar da ka ke ta wannan haukan a kanta, duk matan garin nan? Wallahi ka bani kunya" mahaifiyarsa tayi maganar a ƙule. Aka tambayi ramma sunanta ta faɗa, aka nuna mata Abdul aka ce "Kin san wannan?" Ta jinjina kai alamar eh. "Waye shi?" "Mijina ne" ta faɗa kai tsaye. Gaba ɗaya su ka Kalle ta, cikin takaici mamanta ta ce "A gidan uban wa ya zama mijin naki?" Nabila ta tashi ta je gaban ramma, cikin raɗa ta ce "Dan Allah ki nutsu rahama, ki yi bayanin komai, saboda a ƙwatar miki hakkinki" Aka sake tambayar ramma "Meye alaƙarki da shi, me ya yi miki?" Tayi shiru ta na kuka taƙi magana. Abokin Indabo ya ce "Ni fa ina ga wannan abun duk da masalaha aka yi, aka sasanta abun nan, dan gudun ɓacin sunan yarinyar nan, tun da akwai aure kuma abin nan ya wu.... "Shut up, ba rikicin jam'iyya ba ne ba ko na siyasa, a ƙwatarwa yarinya hakkinta mu ke buƙata" Viper ya yi maganar cikin tsawa. "Aminu Viper, mai bunu a ƙugu ba ya kai gudunmuwar gobara, ka bari ka fara kashe wutar gabanka, kafin ka zage ka na ɗaga jijiyoyin wuya, haryanzu ɗa na ya na da gatan da za a iya shafe ko ma me ya aikata, mu ka zaɓi ayi masalaha". "Gobarar da nake ƙoƙarin kai gudunmuwar kasheta, ai ku ne gobarar, dan kun fi ni shiga matsala da hatsari, a ɗauki statement a gabatar da ƙararmu a gaban kotu " "Ya isa haka, nan fa gaban hukuma ne, ba teburin caca ba. Ke ki yi magana mu na jiranki" Ɗan sandan yayi maganar yana kallon ramma. Da ta ɗaga kai ta kalli Abdul, sai ta ji ta karaya. "Talk" Viper ya daka mata tsawa, ta zabura ta rirriƙe Nabila ta na kuka. A hankali Abdul ya ce "Ku daina yi mata tsawa, yes i rape her, na amsa laifina" "Ba ka da hankali, lauyoyin ka ba su gargaɗeka a kan kar kayi magana ba?" Nabila cikin rarrashi, ta ce "Rahama ki yi magana, dan Allah kar ki bari tausayi ya yi tasiri a zuciyarki, ki yi magana" Cikin kuka ramma ta ce "Ai ya nemi yafiyata, kuma da gani ba shi da lafiya, dan Allah a sassauta masa, ko a bari wataran idan ya warke sai na yi magana". Ayshercool 08081012143 Abu na farko da zamu buk’ata daga wajenka shine mahaifar matarka, Ma’ana ba zaku haihu da matarka ba.” Imaam ya ‘dago yana kallonsa Ya ji kansa ya wani sarà masa, amma sam ya kasa masa musu… Alwan yana murmushi ya ce “Ka kirata ku yi shawara…” Ya fice ya bar masa wajen. Da sauri Imaam Ya kira Safna. Tana d’agawa ta ce “Yaya? Imaam Allah yasa dai baka musu taurin kai ba?” Ya saki huci ka’dan ya furta “Ba zan iya abinda suke so ba….” “Zaka iya Imaam, ka yi koma me suke so? Yanzu fa ba abinda baa yi saboda ku’di, ana ya Kai Kai, mutum yana kwanciyar da y’ar cikinsa, da Uwar data haifeshi ma saboda ku’di, ana luwa’di da ma’digo saboda ku’di, ana bada Uwa ko y’a Yaya ko k’anwa, K’ani ko wa? Duk saboda ku’di, don haka ka yi ko me suke so Moddi Saboda ku’di… bana son musu…” ta fa’da tana zame kanta a duk sunayen da ta ambata, bata k’i ya yi komai ba in dai zai samar musu da ku’di, bata damu ta ji shara’din da suka bashi ba. Imaam Ya saki ajiyar zuciya, sai ya ji ya samu k’warin gwiwar bayar da mahaifarta tunda ita ta jawowa kanta ta ce ya yi komai saboda ku’di. A zuciyarsa Ya dinga jin baya so, amma harshensa ya kasa amince masa ya furta baya so d’in. Ya kalli Alwan da Ya shigo d’akin idanunsa a kansa shima ya ce “Yaya Aboki? Ka yarda ko a’a? Abu guda dana sani baka isa ka San sirrinmu sannan ka bijire mana ba….. Cab’di kin fara bibiya ko har yanzu… Hadarin gabas dai da zafinsa yazo akwai cakwakiya anan gaba… Za’a yi kuka za’a yi dariya za’a sha soyayya a cikin littafin nan. Hanzarta ki fara Ina Imaam Muhammad Moddibo Ya kai kansa? 89 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Sake kallon wayarsa ya yi, ya ga location ɗin wayarta ya na harba hanyar gidan mahaifinta. Kasa nutsuwa ya yi da hakan, kawai ya tashi ya sanya kaya ya fita. Saifu ya riga su Nabila ƙarasawa, Allah ya sa Baba bai kai ga fita ba. Saifu na sanar masa, Nabila ta na hanya, bakinsa ya ƙi rufuwa, ya fasa fita, ya ce a haɗa mata kayan abinci. Ya ce "Saifullahi ita da wa za ta zo nan ɗin?" Saifu ya ce "Itakaɗai ce, kai take son gani" Cike da fara'a ya ce "To Allah ya kawo mini ita lafiya cikin aminci" Ana haka Nabila ta yi sallama, hafsa ta fito da gudu daga ɗaki, ta rungumeta ta na "Oyoyo ga jauhar" Nabila ta yi murmushi ta ce "Nabila dai, ba jauhar ba" ta yi shiru ta na kallon Nabila. "Kin ƙi yadda haryanzu ko?" Ba ta sake cewa komai ba, ta ci gaba da kallon Nabila, ta na ƙoƙarin gano dalilin da ya sanya za ace mata ba jauhar ba ce ba. Baba da kansa ya fito ya tari Nabila, har zuwa ƙaton falonsa, ta zauna su ka sake gaisawa, babu kunya Zakiyya da maman saifu su ka biyo bayanta har ɗakin su ma. Su ma ta gaishe su, su ka amsa su na kallon ta kamar baƙuwar halitta. "Ya ki ke aikin naki?" "Lafiya ƙalau Alhamdilillah" "Ina ɗaya 'yar ta wa?" Nabila ta ce "Ta na wurin aiki, ni ma zuwa nan ɗin faɗo mini kawai ya yi na taho" Ya jinjina kai ya ce "Gaskiya ne, yaushe za ki kammala aikin ne, ki dawo ki zauna tare da ni, in dinga kallonki ina jin daɗi tare da ɗebe mini kewar jauhar" "Baba ko na kammala, zan zo dai na ɗan yauta maka amma ba zan iya dawowa gidan nan na zauna ba, idan na dawo nan gaba ɗaya Abba fa?. Na zo ne na nemi bakin zaren saita tarwatsatsiyar alaƙar da cikinku babu wanda yayi tunanin gyarata duk a sanadiyyar hawa dokin zuciya da ku ka yi. Baba, kai mahaifina ne, major kuma rayuwata ne, kuma ka san waye shi, a fannin tsatstsauran ra'ayi da kafiya, a wannan karon ya sake ɗaukar zafi da yin fushin da har ya nemi ko dai na rabu da kai, da shari'ar mijin jauhar, ko kuma babu ni babu shi, saboda ya na ganin jauhar ba ta samu kyakywar rayuwa daga gareka ba, ka aurar da ita ga ɗan daba, wanda ya yi ajalinta. Tabbas na rayu dogon zamani, cike da muradin son sanin waye mahaifina, sai dai gaba ɗaya na sare, gwiwata ta yi sanyi, tun bayan da na saurari labarin abin da ya faru. Sai dai hakan ba zai hanani sauke hakkina a matsayina na 'ya ba, yanzu warware mini wasu abubuwan, zai taimaka mini a kan shari'ar nan, kuma ya taimaka mini wurin wanke ka a wurin Abba. Dan Allah ka fahimce ni, ba wai ina fatan na ƙure ke ba ne ba, mafita nake nema, saboda ni ce a tsakiya muddin aka ci gaba da tafiya a haka, rayuwata aka saka a tsakiya dukkaninku kuna da muhimmanci a gare ni, kuma babu wanda zan iya zaɓa na bar ɗaya. Dan Allah baba ka warware mini abubuwan da su ka shige mini duhu. Me mahaifiyarmu ta yi maka, ka barota a garin da ba ta da kowa sai Allah sai kai, meye dalilin da ya sanya ka aura wa jauhar mai zamani, duk da ka san waye shi?" Baba yayi shiru, sai hawaye da yake gangarowa daga cikin idanunsa. Zakiyya ta ce "Ke kuwa abin da ya riga ya wuce, menene na gutsura magana, abin da ya faru ya riga ya faru, sai fatan Allah ya kiyaye gaba". Nabila ba ta kulata ba ta ce "Talk please" Ya numfasa ya ce "Nabila, na ga ƙoƙarin ki da ki ka yi saurin saukkowa daga fushin da ki ka yi, ki ka saurareni, kawunki ya yi mini laifi, amma zan iya cewa koma menene ni na janyo. Kuma na so na yi magana da shi ta fahimtar juna, sai dai tsawon wannan shekarun, major bai canza a yadda na san shi ba, yanayin sa ya tabattar mini da ba zai taɓa ba ni dama ya saurare ni ba, tun da amana ce ya bani na ci. Haƙiƙa na so chubaɗo, so na gaskiya, ga ta 'yar ƙauye ba ta da wayewa sosai, amma ina samun nutsuwa da kwanciyar hankali a tare da ita, babu hayaniya ba ta da tashin hankali da kan ƙara, ta na da matuƙar haƙuri da biyayya. Ita kuma zuciya na son mai kyautata mata, hakan ya sanya ko a cikin dangina, ba na ɓoye son da nake yi mata, da na zauna hirarta kawai nake yi na ji daɗi. Ba a iya cikin gidana ba, hatta a yan uwana, sun fara nuna mini cewar ina zaƙewa a kanta, dan sai da aka fara haɗa ni da mariƙiyata a lokacin nan, cewa na tattarare a wurinta, ta yi mini asiri. So da tausayinta ya sanya na ɗauke ta, na tafi da ita garin da nake aiki, saboda ta haihu a tare da ni, na ba ta dukkanin kulawat da ta dace, sai dai daga zuwa hutu, ban san meyafaru ba na manta da chubaɗo gaba ɗaya a cikin kaina ba, na kan yi mafarki da ita, amma da na tashi sai na manta me na gani. Ina yawan ƙoƙarin tuna wani abu mai muhimmanci a tare da ni, amma sai na kasa. Na karɓi transfer ta, na cigaba da aikina, sai watarana da na je azare, ƙanwata ta yi mini maganarta, sannan na tuna da ita, sai dai a lokacin sunanta kawai da ta kira, na ji kamar na kurma ihu, na ji a duniya babu abin fa na tsana sama da chubaɗo, ko kiran sunanta ba na son na ji an yi. Har zuwa lokacin da major ya kawo mini Jauhar, na furta masa sakin chubaɗo ƙasan zuciyata na ƙuna saboda takaici, amma a zahiri ko a jikina. Sai dai na ɗauki soyayyar duniya, na ɗorawa Jauhar, saboda babu in da ta bar chubaɗo a kamanni da kuma haƙuri. Bayan dogon lokaci, kamar wanda ya farka daga bacci haka na tashi cikin tashin hankali, na tariyo abubuwan da su ka faru, na shirya na tafi Jalingo ba tare da sanin kowa ba, na je rigar su chubaɗo. Sai dai mummunan labarin da na iske ya kaɗa ni, wai major ya tafi da ita can in da yake, amma da ita da yaranta duk sun mutu. Ban kawo cewa 'yan biyu bane ku, na yi zaton kawai shirme ne, na mutanen karkara, mussaman su da ba hausa ce ta wadace su ba. Su ka tabbatar mini da chubaɗo ta rasu, dan maitama da kansa ya je ya sanar musu da mutuwarta. Tsananin tashin hankali ya sanya na yi hatsari a hanya, na samu karaya hannu da ƙafa, da raunuka sai da na yi jinya kamar ba zan rayu ba. Na yi kukan rashin chubaɗo, kuma na yi kuka da nadamar abin da na yi. Na bibiyi in da major yake aiki, amma duk wata kafa da zata sada ni da shi ya toshe ta, ban san adadin zuwana Jalingo ba, har a shekarun nan na je, suka ce mini tun da ya je su ka ce masa na je nemansa, har rana mai kamar ta yau bai sake zuwa ba. Waɗanda na ɗan sani a rigar ma duk sun rasu, duk aure-aure na, har yau ban samu mace kamar chubaɗo ba, ita na aura domin soyayya, uwargidana auren zumunta, ta biyu saboda aikina uwargidan da fari taƙi bi na, chubaɗo kuwa soyayya ce ta sanya na aureta". "Au to mu da ka auremu ba dan ka na sonmu ba, ai da sallamar mu ka yi tuntuni, ashe mu zaman kare a karofi mu ke yi" "Aifa tun da mu zaman 'ya'ya mu ka yi, ashe zaman larura ka ke yi da mu wadda ka ke so, zuciyarka take muradi daban" Saifu ya ce "Dan Allah mama menene haka? Duk wannan fa girmanku ba ne ba, abubuwan duk da ku ka aikata duk bai ishe ku ba?" Mama ta ce "Rufe mini baki, kafin na mangareka" Baba ya numfasa ya ce "Tabbas zaman larura, zaman 'ya'ya nake yi da ku, lokuta da dama ba na gane kaina, kawai dai rayuwa gata nan ne dai ina yi. Haka jauhar, akwai abokina sadis Allah ya jiƙansa, shi ya ankare da halin da nake ciki, duk soyayyar da nake yi wa jauhar, ba na iya kataɓus ko da za a dafata a sha romonta, ya ce yakamata na binciki rayuwata, kamar akwai abin da yake damuna. Na ce masa ni ba zan bi bokaye ba, ya ƙyale ni, ya ce mini ba bokaye ba, in nema wa kaina tsari, amma ko a jikina, ni lissafin matan da na tara, da yara yadda zan riƙe su na kula da su, shi ne kawai damuwata in nemi kuɗi. Ga kuɗin akwai su, amma ba na iya morawa jauhar, ina kallonta da yagaggen tufafi, ta na aiki kamar baiwa a cikin gidan mahaifinta amma ba na iya cewa komai. A cikin ƙannena, ɗaya da ta na cikin masu adawa da Chubaɗo, ta kwanta ciwo, na je dubata ta riƙe hannuna ta na kuka take neman afuwata, ta ce mini haushin rawar kan da nake yi a kan chubaɗo ya sanya ta haɗa kai da Maimuna, su ka yi mini asiri, da sunan chubaɗo bayan an yi mana farraƙu, aka zuba asirin a cikin toka, su ka kai cikin ruwa mai tafiya, wai yadda ruwan nan ya tafi da tokar ta ɓace, haka ya tafi da tunanin chubaɗo a kaina. Sannan su ka koma, su ka yi mini sihiri, aka binne a maƙera, yadda ake rura wuta a maƙera, haka zafin ƙiyayyar da na yi mata yake ruruwa a zuciyata duk lokacin da aka kira sunanta. Babu wani mahaluki da na sanar wannan maganar, na haɗiyeta a cikina. Na daina yawon aure-aure dan ba za a bari su zauna ba, sannan duk wadda na aura, ta na da tata kalar matsalar. Wasu abubuwan ba na sanin ana yi wa jauhar, Jauhar ba ta iya tambayata abu, ko kawo mini ƙara. Duk 'ya'yana su na rayuwa kamar yaran sarakai, pant wanda 'ya mace za ta saka, sai na saya, pad ɗin da za su yi amfani da ita ta jinin al'ada, ta na cikin budget ɗin da nake yi duk wata, amma ba na iya magantawa 'yar marainiyar yarinyar da duk cikin yarana babu wanda nake jin daɗinsa, babu mai tausayi da imaninta, amma ba na iya maganta mata komai. Ko da su ka rushe maganar auren jauhar, duƙufa na yi addu'a, haka kurum kuma na ji na karkata na aminta da aurawa jauhar Al'amin. Ko a lokacin da na amsa aura wa Alhaji mu'azzam ita, na amince ne domin ta huta ta samu nutsuwa a can, tun da ni na gaza samar mata da kwanciyar hankali a matsayina na uba, wallahi nauyin laifukan da na aikata ina jin su a tsakiyar ƙirjina Nabila, rayuwa kawai nake yi, amma babu abin da yake yi mini daɗi, mussaman idan na tuna laifukana ga chubaɗo da jauhar, na san ni mai laifi ne, ki nema mini afuwa a wurin Abbanki" Hafsa ta yi wuf ta ce "Wallahi lokacin nan, wani abu aka saka a bakin wata mage, aka binneta da ranta, wai ba zaka ce komai ba, idan aka ce a aura wa jauhar Mai zamani, da maman su saifu, da Anty. Sai kuma Anty da matar gidan su mai zamani, su ka din ga kai ni wurin wasu mutane, ana bani abubuwa wai saboda Alhaji mu'azzam ya aure ni, amma na gaya wa jauhar komai ai, kuma na ce ta yafe mini, jauhar ai na gaya miki duk yadda aka yi, ki ka ce kin yafe mini, amma kar in gaya wa kowa" tayi maganar tana kallon Nabila. Kamar ƙaramin yaro, saifu yake kuka. Zakiyya ta ce "Hafsa ki rasa wanda za ki yi wa sharri sai uwarki, a gidan uban... Maman saifu ta katseta da cewa "Uban waye bai san ki na biye-biyen bokaye ba?" "Idan ma na bi gara ni, a kan ku wanda ku ka haɗa kai ku ka yi wa chubaɗo ai" Nabila ba ta ce komai ba, ta miƙe, ta ɗauki jakarta da wayarta ta na wata irin tsuma, kafin Zakiyya ta yi yinƙurin ba wa Nabila hanya, tuni ta angijeta ta wuce. Saifu ya bi bayanta ya na kiran sunanta, Baba kuwa bai iya motsawa ba, ya dafe fuskarsa ya cigaba da zubar da hawaye. Hafsa zama tayi ta kwanta a jikinsa, ita ma ta na kukan. Zakiyya da maman saifu kuwa kamar za su dambace. Viper ya kawo kai, Nabila ta nufo barin layin, sojan da ya kawota ya biyo ta ya na yi mata magana, amma kamar ta kurmance. Shan gabanta Viper ya yi ya na tambayarta meyafaru. Saifu ne ya nufosu, Viper ya riƙe hannun Nabila. Saifu ya tsaya nesa kaɗan ya na kallon Viper, ya kalli Nabila ya kalli saifu, bai ce komai ba ya ce wa sojan ya ƙaraso da motar su tafi. Babu gardama ta shiga motar, sun fara tafiya ta ce "Wurin Abba za ka kai ni" "Meyasa? Meyasa ma ki ka zo ba tare da kin sanar da ni ba?" Shiru ta yi masa, yanayinta kamar na mai shirin fita hayyacinta. Tsaki ta ja ta ce "Dan Allah ni kawai ka kai ni wurin Abba kawai". "Amma kin san halin da ake ciki ko? Ya za ayi a mayar da ke gida a wannan yanayin?" Cikin kuka ta ce "Ni wurin Abba kawai zan tafi, ji nake ma kamar haukacewa zan yi" Gaba ɗaya tausayi Nabila ta bawa Viper, ya ce "Me za ki je ki yi masa ne?" Ya gyara zamanta ta dube shi ta ce "Viper, shekara ɗai ɗai ɗai shekara ashirin da shida mutum ya na yawon asiri, could you imagine wai asiri aka yi wa baba ya manta da mahaifiyarmu, aka zo ta mutu aka koma kan jauhar, wai abin har da ƙanwarsa kai, jauhar ta yi haƙuri Allah ya sa ta na aljanna, wallahi da ni ce idan ban haukace ba, guduwa zan yi na bar gidan, ko ma na tsani baban namu, ina kallon ka na wahaltawa 'yan uwana amma ni ka tsane ni, Allah sarki manana da 'yar uwata, wallahi kamar haukacewa zan yi Vi, ni kowa ma ya kasa fahimtar halin da nake ciki" tayi maganar ta na kuka ta kasa zama wuri ɗaya. "Kin ga zauna sosai, ai na san me ki ke ji, ni ma ina ji ai" Ta na kuka ta girgiza masa kai ta ce "A'a ba ka ji" "Ina ji mana, ai na fiki sanin jauhar da wacece ita" "Har da matar gidanku wai aka yi asiri, a kan baba ya amince jauhar ta aure ka" Ya ce "Na sani" "To ita meya kawo ta cikin wannan maganar matar gidan naku?" "Ƙawar babar hafsa ce" ya ba ta amsa. Ta marairaice fuska ta ce "Dan Allah abubuwan nan ba su yi mini yawa ba? Gaba ɗaya na rasa me ma zan ce, ta ina zan yi wa major wannan bayanin, ba ma zai saurare ni ba, amma baba abin tausayi ne, gaba ɗaya matan nan sun raina shi, ba su da kirki kai wayyo Allana ni na Nabila, da ma tun ina jaririya tamowar ta kashe ni kowa ya huta" Sai da Viper ya ji kamar ya yi dariya, amma ya gimtse, tabbas Nabila ta na namijin ƙoƙari jaruma ce ta gasken gaske. Kamar yadda ta buƙata, gidan major ya kaita, duk da ya san ya saɓa doka, amma ta na buƙatar yin abin da zai sakata nutsuwa. Mamaki ne ya cika 'yan gidan, ganin Nabila a gidan. "Me kuma ya kawo ki gidan nan?" Ba ta saurare su ba, ta nufi ɗakinta, wasu daga kayan Sauda ta gani a ɗakin, har an gaje mata ɗakin. Kamar mahaukaciya, ta fara watso kayan waje ta na huci. "Ke Nabila wai meye haka ne? Ba an ce kin gano ubanki ba, uban me ya dawo da ke gidan nan kuma? Ko ba kin zaɓi wasu daban a kan shi wanda ya yi wahala da ke ba ne?" Mama tayi maganar ta na haƙiƙancewa. Baba magajiya ce ta shigo da sauri, ta rungume Nabila cikin farinciki. Nabila ta ce "Baba magajiya, finally na ga abbana, sai dai 'yar biyuna Allah ya yi mata rasuwa" Baba magajiya ta ce "Alhamdilillah, Allah ya ƙara tabattar da nasara" "Ki zo ki fice daga gidan nan, kin tafi mun huta, kin sake dawowa ki koma gidan ubanki mu ma mu sakata da mu huta da yaranmu" Nabila ta ce "Ai ni da ke samamkal, duk ba gidan ubanmu ba ne ba, har gara ni na da ke" Mama ta ce dole sai Nabila ta bar gidan, tun kan Major ma ya dawo ya ganta. Baba magajiya ta ce "Da dai kun yi haƙuri ya dawo ɗin, tun da babu wanda ya san abin da ya dawo da ita". Sauda ta ce "Ki rufewa mutane baki, 'yar karere kawai, ke ma kamata yayi ai ki tattara komatsanki ki bar mana gida, tun da amfaninki ya ƙare" Sosai faɗa ya kacame, Nabila ko a jikinta, ta gyara ɗakinta tas, ta nemi mukullin motarta ta rasa, kai tsaye sashen Abba ta nufa, ta nemo mukullin motarsa ɗaya, ta fito. Duk yadda su ka yi ƙoƙarin hanata ɗaukar motar su ka kasa, saboda yadda su ka lura da fuskarta babu mutunci. Gidan Gonar Major ta nufa, ta na ta zabga addu'a domin ta yi nasara a kansa ta samu ya saurareta, dai dai su ka yi saɓani, domin kuwa baya nan. Su na tsaye su na ta mayar da yadda aka yi, su ka saka baba magajiya a tsakiya, su na kiranta da munafuka. Cikin rashin jin dadi Walida ta ce "Bai kamata ba baba magajiya fa dattijuwa ce, kuma ba ta san komai ba" "Dalla rufe wa mutane bakinki a wurin" Sallamar Major ce ta sanya su ka yi shiru. "Meyafaru ake waye munafuki menene?" Cike da ƙwarin gwiwa mama ta ce "Wai Nabila ce ta dawo gidan nan" Ya ce "To sai aka yi yaya?" "Ai abin ne da mamaki, duk dambarwar da aka yi babu kunya ta dawo gidan nan, motarka fa t ɗauka ta fita, ni dai na ce bar gidan nan kafin ma ka dawo ka tarar da ita". Ya kalli mama da ta haƙiƙance, ya ce "Saboda tare mu ka haɗa kuɗi mu ka gina gidan?" Turus ta yi ta na kallonsa. "Ina ruwanku da ita?" Sauda ta ce "Amma Abba, abubuwan da ta yi maka fa, kuma kai ka ce kar ta dawo maka gida, muddin ba ta yi abin da ka ce ba... "Ni na gaya miki haka? Idan ma hakan ne na naɗa wani wakili a cikinku ne da na ce idan ba na nan a yanke hukunci makamancin wannan?" Su ka yi tsuru-tsuru. "Duk in da za ta je ta san ba ta da kamar nan, ciki har da gidan uban na ta, ni nake da ikon sallamarta ko na ƙyaleta a gidan nan, duk in da za ta je ta dawo, babu ruwanku da ita" Sauda ta ce "Amma Abba ta ɗauki motarka" "Eh ta wace ai, ba wani abu" yayi maganar dai-dai lokacin da Nabila ta shigo. Su ka yi kallon kallo da Abba, ya wuce ya nufi ɗakinsa, bin bayansa ta yi ta na kiran sunansa, amma ya yi mata shiru. Sai da ta dangana har bedroom ɗin sa, wanda a nan ya tsaya, ya juyo ya kalleta bai ce komai ba. "Abba" ya kalleta. "Abba dan Allah ka yi mini magana mana, ko zan samu ƙwarin gwiwar sanar maka da abin da na zo maka da shi. "Kin gama fushin kenan?" "Abba ka fahimce ni, ka yi mini uzuri dan Allah. Na kasa sarrafa zuciyata ne a wannan lokacin, ka yi mini uzuri ni ma 'yar uwata na rasa. Na je wurin baba mun yi magana ne, dan Allah Abba. "Stop it please, in dai maganar mahaifinki ce ba na son jin komai menene, sannan ki je ki cigaba da kare wanda ya kashe 'yar uwakki saboda rashin kishin kai". "Abba ba shi ya kasheta ba... "Ba shi ya kasheta ba ke ce kenan? Azzalumin mutumin nan, bayan kashe mini 'yar uwa, yar da ta bar masa ma, ya kasa riƙeta babu abin da za ki gaya mini a kan mahaifinki na yarda Nabila, Kodayake laifina ne, da na kai masa ita, ni dama ke na kai". Jiki a sanyaye ta ce "Abba... "Get out Nabila, ba na son ganinki ma, fita ki bani wuri" ta haɗiye wani abu mai mugun ɗaci, ta fice daga ɗakin nasa. Ɗakinta ta tafi, kawai ta nemi wuri ta kwanta, baba magajiya ta kawo mata abinci, amma ta ce ba zata ci ba. Washegari da sassafe, Viper ya isa ƙofar gidan su Nabila, ya tsaya ya na kiran wayarta, Nasir ya fito da motarsa. Bai kula shi ba ya ci gaba da kiran Nabila, ta ɗaga ya ce "Ina waje" mintuna kaɗan ta fito cikin shirinta na fita aiki. "Ina kwana" "Lafiya ƙalau, ba wata matsala dai ko?" "Akwai mana, meyasa za ka tambayeni, kai ma ka san akwai muje kawai" Wani irin azababben kishi, ya turnuƙe Nasir, ya fito daga motarsa ya tunkaro su. "Nabila, ki na nufin kin fifita son zuciyarki a kan abin da Abba ya gaya miki?" Nabila ta ce "Mu ƙaddara haka ne, meye naka a ciki?" "Mutumin da ya kashe 'yar uwakki, haryanzu ki na kan bakanki na kare shi kenan?" "Kai ma da ka samu dama, kashenin za ka yi, domin cikar naka muradin. Yaya Nasir kallonka kawai nake yi, kuɗin da aka baka domin ka kama shi, wasa da rayuwata da ake yi, ba tare da ka sanar mini ba, ko ƙoƙarin bani wata cikakkiyar kariya ba, duk fa kallonka nake yi" saroro ya yi ya na kallon Nabila. Viper ya riƙe gefen kwalar Nasir, ya risunar da muryarsa ya ce "Kar ka manta, ni ba karabutin ɗan daba bane kawai, hatta evidence na kuɗin da aka baka, ina da shi. Dan haka ka ajiye kishi a gefe sauran mutuncin da ka ke da shi a idonta ya zube. Nabila ta wa ce, ko da kuwa ita ma zan kashetan ne" Nasir ya kalli idon Viper, Viper ya kalle shi. "Na fi ka gwagwarmaya da ganin wahalar rayuwa, dan haka ba wani zare ido, da wani abu makamancin haka da zaka yi mini da zai tsorata ni. Ka daina shiga harkata dan ka ganni tare da ita, idan ka ci gaba kuma abin da zai biyo baya ba zai yi mana daɗi ba". Tsagwaron kishi ne yake damun Nasir, kamar zuciyarsa zata tarwatse haka ya na kallonsu, suka hau mota su ka tafi. *** Abbu ya na zaune ya na ta lissafi na shekara, nawa zai fid da zakka da sauransu. Hankalinsa ya yi zurfi sosai a tunanin. Rahila na gefe ta na ta yi wa shahida masifar, an raba auren su, ta dawo gida su na haɗa kafaɗa. Shahida ta ce "Auren da da shi, gara babu, ni wallahi ba na dana sani". "Ai dama ba zaki yi ba, nan gaba za ki fahimci abin da nake gaya miki" Wayar Abbu ce ta fara ringing, sai da ta yi sau kusan uku, sannan ya ɗaga. Jin muryar babban mutum ya sanya ya nutsu, su ka gaisa. "Daga nan hedkwatar hukumar hisba ne, mun kamo 'yarka a cikin sabon gari, shekranjiya da daddare, kuma a binciken da aka yi, an gano ta na ɗauke da juna biyu, kuma ga cutar ƙanjamau, dan haka mu na buƙatar ka zo mu na son ganinka" Abbu ya ce "Ba ni ne mahaifinta ba, ta baku lambar babanta ba ni ba ne ba" ya gama wayar, Rahila ta ce "Na ji ana maganar hisba, ka ce ba kai ne babanta ba" Ya ce "Eh, 'yar ki da ki ka ce mini ta na gidanku, ita aka gano a sabon gari, da ciki da kuma ƙanjamau, dan haka na ce a nemi mahaifinta ba ni na haifate ba" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, na shiga uku na lalace, ciki da ƙanjamau kuma? Wayyo Allana" Tashi ya yi ya fice ya bar mata falon. *** Garden ɗin da suke haɗuwa da Nabila a da, can su ka tafi. Ta kalle shi ta ce "Meyasa ka kawo ni nan" "Ina jin nishaɗi idan na zo irin wurin nan, sannan wuri ne mai sanya nutsuwa, ki ɗan huta kawai" wani irin daɗi ne ya ratsa Nabila, ganin yadda ya nuna damuwarsa a kanta ƙarara, sai dai ta basar da ta tuna alƙawarin da ta ɗauka. Hannunsa riƙe da leda su ka ƙarasa cikin garden ɗin, ta zauna ƙamshin furannin wurin na ratsata, haka kurum ta ji zuciyarta na narkewa da ƙaunar mijin 'yar uwatta ta, da take ganin kamar ba ta kyauta ba cin amana ne yin hakan. "Vi" "Abla" "Abba yaƙi fahimta ta, ya kore ni, ya ce muddin ina son zaman lafiya, to sai na bar shari'arka, na rabu da mahaifina". Viper ya gyaɗa kai ya ce "Ya ɗauki zafi da yawa ne, amma zai saukko, ba ya bari kin kwana a gidan ba?" "Eh, jiya da na dawo ma na tarar ya na faɗan babu ruwansu da ni, ina ga so su ka yi ya kore ni ma, duk sun gaje mini kaya, har da motata" Ya ce"Sorry" Ta numfasa ta ce "Ka na addu'a kuwa, a kan Allah ya bamu sa'a?" Ya ce "Eh, ina yi" "Masha Allah, amma fa dole mu ƙara, kuma ka yi haƙuri dole za mu yi exposing wasu abubuwan da ka yi a kotu" Ya ce "Kamar yaya? Ba dai aikina ba?" Tayi murmushi ta ce "Ba wannan ba, rashin jin da ka yi, da alaƙarka da indabo, ka san babban kuskuren da ka yi? Biye wa Nura guduma da ɓoyewa likitoci ainihin abin da ya same shi. Da sun yi documenting hakan zai bamu ƙwarin gwiwa da cikakkiyar hujjar dalilin da ya sanya rigima tsakaninka da Indabo. Yanzu dole abin ɓoye ya fito fili, muddin lakwari ya kuma denying kashe jauhar, shaidar ɗan mama kaɗai ta yi rauni, dole duniya ta san da videon nan". "Ki na nufin Videon Nura? No ba zai yiwu ba, cin amana kenan da karya alƙawari". Ayshercool 08081012143 90 Ta girgiza kai ta ce "Ba ina nufin lallai sai videon ya fita ba ne ba, ka fahimce ni. Indabo sun san me muke shirin yi, ba fa za su ƙyale mu ba, bar ganin hankalinsa ya na kan ɗan sa da kuma tuhumar da ake yi masa, ya na da muƙarrabansa, ya na da iyayen gidansa da waɗanda siyasarsu ta dogara da shi, ba za su taɓa zuba ido su na kallonmu ba. Duk wani tanadi da shiri da yakamata mu yi, dole mu yi shi, ko da kuwa ya na nufin faɗar abubuwan da ka aikata. Dan ba kowa ne zai ɗauki cewar akwai wata alaƙa tsakanin ɗan daba da mutum kamar sanata ba, har ta kai ga ya kashe maka mata ba. Dole sai mun shirya da shaidu da hujjoji fa, ba da ƙanan lauyoyi zan kara ba, na sani manyan lauyoyi ne iyayena a harkar aiki, muddin aka kai ga gaɓar da sunan Indabo zai fito a cikin shari'ar nan. To fa tsuguno ba ta ƙare ba, dan  haka kurum su lakwari ba za su kashe maka mata ba, kuma dole za su yi ƙoƙarin kare kansu, ko mu bamu faɗa ba, su za su iya faɗar wasu abubuwan da suke da alaƙa da ka yi daba da kuma dillancin miyagun ƙwayoyi, wanda laifi ne ga dokar ƙasa, da za na iya fuskantar tuhuma" Viper ya yi shiru jikinsa a sanyaye ya ce "Da sauran rina a kaba kenan? haryanzu ban gama karɓar sakamon laifukana ba kenan" yayi maganar cikin damuwa ya na ɗan murza zoben hannunsa. Cikin kulawa da matsanancin tausayin sa ta ce "In sha Allah komai zai warware, ai babu abin da ya fi ƙarfin Allah, kuma shi mu ke gaya wa. In sha Allah abubuwan da su ka faru, kaffarar laifukan ka ne, in sha Allah sai an tuhumi indabo a kan mutuwar jauhar, muddin sunan sa ya fito a kotu, to shi ma za mu yi ƙararsa ne, fatana Allah ya bamu nasara" yayi shiru ya na tunani. "Vi" ta kira shi a hankali. Ya ɗaga kai ya kalleta amma bai yi magana ba. "Ka ce wani abu mana" "I have nothing to say" "Idan ka karaya ni fa? Dan Allah ko yaya na ga alamar ƙwarin gwiwa a tare da kai mana, kar ka saka na karaya mana Please" ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Duk mai nema, dole ya sanya rai a samu ko rashi, duk wanda ya riske ni, zan karɓa da murna na gode wa Allah" "Duk da haka, yakamata bawa ya kyautatawa Allah zato, burina ɗaya tak ya rage a duniya da nake fatan cika shi, shi ne ƙwato muku hakkinku, da kai da jauhar, ko da hakan ya na nufin ƙarshen rayuwata. Ina ta gudanar da bincike na a ɓoye, ina tattara bayanai, hatta report ɗin likitoci a kan mutuwar ta, ina processing na karɓa. Alhaji mu'azzam ya na taimaka mini sosai da sosai" Nan da nan annurin fuskar sa ya ɗauke, rai a ɓace ya ce "Shi kuma me ya kawo shi cikin wannan maganar?" "Komai ma mana, ka san abubuwa da yawa ban da taimakon Allah, ya sanya ya na tare da mu ya na taimaka mana, da tuni an kaimu ƙasa an ga bayanmu, bawan Allah nan ya cancanci yabo wallahi" banza ya yi mata yaƙi yi mata magana. "Ni idan Allah ya sa aka kammala shari'ar nan, lallaɓawa zan yi na yi aure, su Baba idan za su shirya da major to, idan sun ƙi ina ɗakin mijina ina yi musu addu'a Allah ya yafe musu ya sanya su gane" "Amma kin manta mijin 'yar uwakki ne?" Nabila ta ce "Na sani mana, dama ba jauhar ya fara so ba? Kuma ai yanzu ba ya tare da hafsan idan ba zai mayar da ita ba ni sai na aure shi, ko na auri barrister Habib, ko ma duk wanda Allah ya sa ya samu, Allah ya zaɓa mini mafi alkhairi ya bani wanda zai kula da ni" ta na cikin maganar ya miƙe ya bar wurin. Tashi ta yi ta bishi, amma har su ka shiga mota su ka fara tafiya bai kulata ba. "Vi ka yi haƙuri idan laifi na yi maka mana, ka wani haɗe rai ka sha kunu kamar boss" gefe ya ci gaba da kallo. "To ni dai yanzu ba tsoronka nake ji ba duk muzuran da za ka yi mini, da dai na fi jin tsoronka" ya juyo ya yi mata wani irin kallo, take ta tsuke bakinta ta ce "Am sorry". *** Ramma laulayi ya sakata a gaba, ba ta iya cin abinci, komai ta ci sai amai, duk da ƙasan zuciyar mahaifiyarta babu daɗi ta na tausaya mata, amma a zahiri yadda rammar ta fifita abin da take so, a kan cin zarafin da aka yi musu, ya fi komai baƙanta mata rai, da ta tuno hakan sai ta ji ranta ya ƙara ɓaci. Alhaji mu'azzam ne ya je gidan, duba su ramma, su ka gaisa. Ya ce "Hajiya ku yi mini uzuri fa, ayyukan ne da yawa sosai sai godiyar Allah, kwana biyu ban samu na leƙo ku ba" Maman ramma ta ce "Wallahi babu komai Alhaji, ai muke da godiya Ubangiji Allah ya ƙara arziki ya sanya a fi haka" Ya ce "Amin, mun yi magana da Nabila ta ce babu wata matsala, amma ya na ga rahaman kamar a cikin damuwa ne?" "A'a babu komai, kawai dai ba ta jin daɗi ne" "An je asibiti ne?" "Eh lafiya lau". Ya ce "To Alhamdilillah ai Nabila ma ta ce mini ta na hanya, ina son jin ya ake ciki, zuwa yanzu yakamata ace ai an fara shari'ar, tuni a tura shi prison" gaban ramma ya faɗi, duk yadda ta so ta takura zuciyarta ta ji ta tsani Abdul a yanzu kasawa take yi, tausayinsa ya kanannaɗe mata zuciya baki ɗaya. Ba a jima ba sai ga Nabila ta iso, Ramma na ganin Nabila ta ji farinciki ya mamayeta, saboda itakaɗai ce take fahimtar ta, take lallaɓata ba tare da ta ƙosa ko ta hantareta ba. Duk su ka gaggaisa, Alhaji mu'azzam ya ce "Barrister ya ake ciki ne? An ce an ɗauki statement da komai, me ake jira ba a gurfanar da shi a gaban shari'a ba?" Nabila ta ce "Eh na je na tuntuɓa, ina ta bibiyar lamarin shi Abdul ɗin ba shi da lafiya sosai, haryanzu ya na fama, ya na kwance a asibiti ma, ya na karɓar treatment. Duk ina son na je na duba shi, dan na tabattar" "Yakamata, ki je da kanki, kar ayi wata cuwa-cuwar ko kuma ƙarya yake yi" "A'a ba ƙarya yake yi ba, ba shi da cikakkiyar lafiya dama" sai kuma ta yi saurin tsuke bakinta, ganin duk sun waiwayo su na kallonta, musamman mama da ta galla mata wata uwar harara. Kankarofi ya ce "Too, ikon Allah me yake damunsa haka?" Ta ɗan saci kallon mama, jiki a sanyaye ta ce "Ciwon ciki ne mai zafi" Ya ce "To Allah ya bashi lafiya, ayi Shari'ar nan, a ƙwatar miki hakkinki da ke da mahaifiyarki" Nabila ta juya harshe zuwa turanci, ta ce "Yallaɓai, ina tsoron yin shari'ar nan yarinyar nan ta bamu kunya, wallahi ta na son mijinta, daga ita har shi su na son junansu" Waro ido ya yi ya kalli Nabila ya ce "Haba dai?" "Ka ga abin da su ka yi a station kuwa? Ga mutuminka ya ɗauki zafi a kan lamarin nan, ka san fansa yake so ko ta halin ƙaƙa, a zuciye yake da su, nayi-nayi ya ƙi fahimta, ka san ba ta da wani tsayayye yanzu idan ba shi ba, ya kafe ya dage, dan kamar zai daketa, ga ciki kuma na rasa yadda zan ɓullowa lamarin nan" Kankarofi ya jinjina kai ya ce "Lallai akwai ƙura, to dama ni nawa support ne, na yi supporting ɗin ku, financially na baku security, decision kuma wannan naku ne, Ubangiji Allah ya bayar da sa'a duk abin da ku ka yanke, ni dai-dai ne a wurina" Nabila ta ce "Shikenan, hakan ma mu na matuƙar godiya, Allah ya saka da alkhairi ya sanya a fi haka" Ya amsa da "Amin Barrister, ai aikinki ya na kyau Ubangiji ya ƙaro mana irinku a cikin al'umma, kin sake komawa wurin mahaifinki kuwa, na je masa sau ɗaya, haryanzu ina jin nauyinsa ne abin da nayi". "Kar ka damu, ai ba mutum ne mai damuwa ba, iyaka idan ka na buƙatar ya dawo maka da matarka ne shikenan, sai na tayaka biko" ya ɗago ya kalli Nabila ya yi shiru, sai kuma ya miƙe ya tashi ya yi musu sallama. Nabila ta ce "Rahama, ki na cin abinci kuwa duk kin rame" Maman tayi caraf ta ce "Ina fa za ta ci, ta ɗauki soyayyar ɗa namiji ta saka a zuciyarta, ba ta tausayina ba ta kallon a masifar da ya saka mu a ciki wata da watanni ina yawon yadda za ayi na ganta, hankalina a tashe" A marairaice ramma ta ce "Mama ya ce nemanki yayi ya rasa, shiyasa bai dawo da ni ba, saboda za a iya kashe ni, dan a kare shi kuma wallahi ni ba soyayyarsa na saka a raina ba, a kan me zan so wanda ya keta mini haddi" "Rufe mini baki, ko na zaune ki, soyayyata ki ka saka a ranki ai ko? Tun safe yanzu sha ɗaya na safe, ba ki fito kin nemi abin karya ba, ki na kwance ki na tunani" Nabila ta katse hirar da"ba zai yiwu ba, tashi mu je ki dafa abinci da hannunki, mu fita shan iska, kya samu ki huta ke ma" Ta saka ramma a gaba, su ka shiga kitchen, ta ce mata ita ba ta son ko ƙamshin abinci, ita ba za ta iya cin komai ba". Nabila ta ce "Dubiya za mu je, mijinki ya ce lallai ya na son ganinki, idan kuma ba kya so shikenan" ai babu shiri ramma ta zage, ba tare da ta san tayi hakan ba, ta yi girki, zuwa azahar su ka yi salla, Nabila ta ɗauke ta su ka fice. Har asibitin da Abdul yake su ka je, jami'an tsaro na ƙofar wurin a tsaye. Nabila su ka shiga tare da ramma, ƙirjinta sai dukan uku-uku yake yi. Shi da wani su ka tarar da shi, su ka gaisa da mai jinyar wato Salim wanda abokinsa ne kuma ɗan uwa dan su na da alaƙa, Nabila ta ce "Lauya ce ni, ko za ka iya bamu wuri for some moment" ya ƙarewa Nabila kallo, ya ce "Na gane ki ai" daga haka ya tashi ya fice. Abdul ya na kwance, ya na bacci, ya na sanye da wando 3quater da vest, fuskar nan ta yi fayau saboda ciwo. Ramma har tsuma take yi, ta na bin sa da ido. Nabila ta ce "Bari na je waje na jira ku" ta fice daga ɗakin ita ma. Kamar jira take Nabila ta fita, ta ƙarasa da hanzari ta saka hannu ta riƙe hannunsa ɗaya, ɗayan kuma ta ɗan jijjiga shi ta ce "Doctor, Abdul tashi ni ce" a hankali ya juyo, ya buɗe ido, da sauri ya kalli ɗakin ya kalleta ya ce "Rahama, ke ce ya aka yi ki ka zo nan?" "Anty Nabila ce ta kawo ni" "Wannan lauyar ta ki?" Ta jinjina masa kai alamar eh. Abdul ya ce "Ai na ga kamar ta na da tausayi, ba kamar wannan mai zamanin ba mara imani" Ramma ta ce "Yayana ne fa, shi kuma yar uwar matarsa ce, yan biyunta ce" "Ke ma kin san ba shi da kirki, ko tausayinmu ba ya ji, am missing you sweetheart" yayi maganar yana janyota jikinsa. Luf ta kwanta a ƙirjinsa, ta ce "Ya jikin naka?" "Wallahi ba zan ɓoye miki ba, babu sauƙi, ni kawai a kaini kotun, idan a can prison ɗin zan mutu shikenan, idan ina da rabon na rayu, gara ayi a kai ni na fara lissafin shekarun da zan yi" Cikin rauni ta ɗago ta kalleshi ta ce "Dan Allah ka daina cewa zaka mutun nan, idan ka tafi binka zan yi, ko bacci ba na iya yi, na rasa abin da yake yi mini daɗi" "Dan Allah da gaske rahama? Ki na so na kenan? Wallahi ciwon nan nawa har da damuwa, hepatic tuberculosis  ke damuna, TB ta kama mini hanta, ikon Allah ne kawai zai saka na rayu, saboda shaye-shayen da na yi ne na san ya haddasa mini hakan" Ramma ta ce "Zaka rayu in sha Allah, ka daina irin wannan maganar, ka na karya mini zuciya" tayi maganar tana hawaye. Ya tallafi fuskarta, ya ce "Rahama dan Allah kan na mutu ki ce ki na so na, ko sau ɗaya ne" "Wai ba zaka daina zancen mutuwar nan ba, wallahi zan daina zuwa idan za ka din ga wannan maganar" Ya ce "To na daina" Ta goge hawayenta ta ce "Ga abinci na kawo maka, ai za ka ci ko?" "Ba na iya cin abinci, amma tun da ke ki ka kawo, dolena na ci ai, your excellency rahama Abdul yasar" Murmushi ta yi, ta ɗaukko flask, ta zauna a kusa da shi, ta fara ɗebowa ta na kai wa bakinsa. Ci yake yi ya na kallonta, ba zai iya misalta abin da yake ji a kanta ba, na soyayya. Hannu ya saka ita ma ya na bata, sai su ka so manta halin da suke ciki. Ta gama, ta raka shi banɗaki, ya yi alwala, ya dawo ya zauna ya tayar da salla. Duk abin nan Nabila na zaune ta na danna waya, ta yi shiru ta na kallon ƙofar ɗakin, da alama ma sun manta da ita ne a wajen, ta jinjina kai lallai mata da miji sai Allah. Ban da Abdul ya na da gata, ya za ayi ma a kawo shi wannan asibitin jinya, kamar ma ba wanda ake tsare da shi ba. Nabila na ɗaga kai ta hango babar Abdul na tahowa, tare da security ɗin ta, hannunsu da fulasai. Abdul kuwa bayan ta gama ba shi abinci, sai ya marairaice wai dan Allah ta yi masa wanka, wai da kansa yake yi, baya bari kowa yayi masa, kuma idan yayi baya fita. Ya lallaɓata da daɗin baki, ta saɓa hijjabinta, su ka tafi toilet. Maman Abdul na zuwa Nabila ta tashi, ta ce "Sannu da zuwa, bari ayi musu knocking tukuna, ya na da baƙuwa ne" kallon banza ta yi wa Nabila, kawai ta buɗe ƙofar ɗakin. Abdul ya na kwance ruf da ciki, ta yi masa wanka, ta na shafa masa man zafi a bayansa. Tashi ta yi cikin tashin hankali, ramma ta ja da baya, ta na zazzaro ido, tare da ƙoƙarin sanya hijjabinta. "Me zan gani haka, wannan matsiyaciyar yarinyar har asibiti me ki ke yi a nan, ke wace irin 'yar isaka ce ne?" Abdul ya ce "Mummy ba 'yar iska ba ce, mata ta ce fa" "Rufe mini baki ko na ɗauke ka da mari" Nabila ta ce "Hajiya, ba ramma ce ta kawo kanta ba, shi ya nemi ya ganta ta hanyar lauyansa, su ka roƙi alfarma na kawota, amma ba 'yar iska ba ce" "Rufe mini baki, banda munafunci, kun haɗa baki a kan lallai sun kun kassara mini iyali, kun dage sai kun kulle mini ɗa, kuma saboda iskanci kin kawota ta na yi masa karuwanci, ƴar ƙanƙanuwa da ke kin iya bariki" "Mummy dan Allah ki daina aibata mini mata, wane irin karuwanci fisabilillahi. Ni fa ina buƙatar matata a kusa da ni" Ta ƙarewa ramma kallo, ciki ne a jikinta ya fara tasawa. "Me nake gani a jikinta kamar ciki ma? Amma dai ba na ka bane ko?" Abdul cikin damuwa ya ce "Dan Allah Mummy ki daina aibata mini mata, ba dan ni ba, ina son matata, idan laifi ne na yi musu laifi, dan Allah ki daina aibata mini ita, ina jin zafi sosai" galala ta buɗe baki ta na kallon Abdul. Nabila ta ƙarasa ta danƙo hannun Rahama, ta ce "Zo mu tafi" Riƙeta Abdul ya yi, ya na yi mata magana ƙasa-ƙasa. "Na gode sosai da sosai your excellency tun da aka kama ni, ina cikin baƙin ciki da damuwa, amma na yi farinciki sosai da sosai, na gode rahama. Allah ya saka da mafificin alkhairi, ki cigaba da yi mana addu'a" Jan shi mahaifiyarsa take yi, amma ya yi ƙam da rahama, ya na yi mata magana a kunne. Jinjina masa kai kawai take yi, idanunta na cika da hawaye. Hankaɗe ramma ta yi ta na ce mata munafuka, Nabila ta riƙe ta, ta kalli maman Abdul ta ce "Ki bi a hankali, wannan zafafa ƙiyayyar ba naki ba ne ba, rayuwar ɗanki na hannun Allah ta na da alaƙa kuma da Rahama, duk wannan fusatat da ki ke yi akwai rabo a tsakanin su, gara ki kwantar da murya ki lallaɓata da iyayenta, dan wannan abun da yake yi a kanta, ba soyayya ce kawai ba jarrabawa ce". "Wallahi ƙarya na bi matsiyata yan ƙauye ina roƙonsu, shi ma asiri su ka yi masa" Nabila ta ce "Idan ke ba ki bi su ba, shi gashi ya lalace ai a kan yar ƙauyen" "Ke ki iya bakinki ko na kifa miki mari, na saka ayi dukan tsiya" "Barrister ce ni, tsaf hakan zai saka ke ma a yanka miki tikitin tafiya in da mijinki da ɗanki ke shirin tafiya". Ramma kuka kawai take yi, Abdul kuwa ya kasa magana, sam bai ji haushin abin da aka yi wa mummyn ba, shi matarsa ce kawai damuwarsa. Nabila su na tafe a hanya, ta ce "Rahama za ki iya yafe wa Abdul yasar?" Ramma ta kalli Nabila amma ta yi shiru. "Ki na son mijinki ko?" Still shirun ta yi ta na wasa da yatsunta. "Ki gaya mini masalaha nake son a nemo" "Ba na son shi, kawai tausayi yake bani" Nabila ta yi murmushi ta ce "Rahama kenan, menene son menene tausayin, ki na tsoron abin da zai biyo bayan amsar da zaki bani ne kawai. Abin da ki ke so dole shi za ayi, idan ki na son mijinki, ki gaya mini a nema masa sassauci ko ma ki yafe masa, ku yi rayuwar aurenku, na san yadda zan ji da Mama da Vi" Ramma dai ta yi shiru, ba ta iya cewa uffan ba. Tunani ta tsunduma, yadda suka kasance tare yau tare da Abdul, "Dan Allah rahama kar ki bawa kowa zuciyarki har na fito, zuciyarki tawa ce nikaɗai" "Ba zaka yi shiru ba, sai na saka maka sabulun nan a baki, da kyar ka ke magana sai haki ka ke yi" Ya marairaice ya ce "Dan Allah ki bar mini zuciyarki" "Nawa zaka saya?" Yayi murmushi ya ce "Ai darajar zuciya, ba a iya musayarta da komai, sai zuciya 'yar uwatta" "Ji yadda ka ke magana, kamar a film juya ko na zuba maka dundu ni" Ya lumshe ido ya ce "Dundun ƙauna ne" murmushi ne ya suɓucewa ramma, ba tare da ta shirya ba, Nabila kawai ta kalle ta, ta girgiza kanta. A falo su ka tarar da Viper, fuskarsa babu rahama babu annuri, tuni Ramma ta tsure, Nabila kuwa ta sha jinin jikinta. Cikin dakewa ta ce "Vi sannu da zuwa, dama zaka biyo nan ne? Na zata tafiya kawai ka yi" Miƙewa ya yi tsaye ya ce "Daga ina ku ke?" "Amm...mm" ganin ta na neman ƙaryar da za ta yi masa ta kare kanta, ya sanya shi ɗago mata wayarsa. "Duk in da ki ka je ina gani, kuma na jira Emanuel, ya gaya mini in da ya kai ku, Me ki ke shirin yi ne, me ki ke shirin aikatawa? Are you human being, kamar ba mace ba? Idan ita ba ta da hankali ke fa? Dan me za ki ɗauke ta ki kaita wurin wannan ɗan iskan yaron? Me ki ke shirin aikatawa ne? Yadda da na yi da ke ya sanya nake jin za ki iya ragamar komai yadda ya dace, amma na rasa in da ki ka dosa. Ko ke ma kin sauya layi daga in da na sanki, ta kanki su ka biyo kenan saboda case ɗin ya sha ruwa? Rahama ba za ta taɓa zama da wannan yaron ba, kuma dole a hukunta shi" Maman rahama ta ce "A'a Aminu, a bi komai a hankali, ta na ƙoƙari ai" Nabila ta kalli ramma ta ce "Jeki abinki rahama, Allah ya huta gajiya" Ta kalli Viper ta ce "I so much respect humanity, yardar da ka bani, yanzu babu ita ka na doubting a kaina, saboda kawai na kai rahama wurin mijinta. Idonka ya rufe fansa ka ke so ko ta halin ƙaƙa shiyasa ka ke son sai an hukunta Abdul da laifin da ya yi da wanda ba na sa ba. Hukuntaka da aka yi da laifin da ba naka ba ya sanya na tsaya kai da fata, tun ban san ina da alaƙa da kai ba, a kan ƙwato maka hakkinka. Ko hukunci za ayi, iya laifin da Abdul ya yi kawai za a hukunta shi da shi. Ina rashin karɓarka da al'umma su ka ƙi yi a lokacin da ka ke buƙatar su, shi ne musababbin sake shigarka mawuyacin hali? Da na ƙyamace ka, ko na gujeka da a wani stage ka ke yanzu? Kar ka manta har yinƙurin kashe ni ka yi ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba, an nemi rayuwata wuri daban daban saboda kai, amma hakan bai sanya na haƙura na ƙyaleka ba. Kar ka manta a yadda ka ke, aka ɗauki auren 'ya aka baka, shikenan mutum ba zai yi kuskure ya tuba a karɓe shi ba, sai a ɗauki laifin nasa kawai a saka a gaba. Zunzurutun kuɗi miliyan nawa ya kashe a garinku, kuɗin da a sanadinsu, ubansa ya na can ya na fuskantar tuhuma, ya biya kuɗin makarantar ramma har jami'a, kuɗin rainon cikinta da abin da za ta haifa, hatta kuɗin kula da al'amuransu na yau da kullum ya bayar, duk dan ya wanke laifin sa,ni da ku mun san banda ƙaddara rahama ba ta isa zuwa in da Abdul yake ba, son da yake yi mata jarrabwa ce kawai. Ban da an tsaya mana mu ma, Abdul  ya na da gatan da za a iya sakinsa, kawai dan mun samu manya sun shiga abin ne, amma ya zaɓi a hukunta shi, muddin rahama za ta yafe masa. Mama ke ma fa uwa ce, kuma Allah ya taɓa Jarabtar ɗanki da kauce hanya, ke ki ka zaɓa masa zama hakan? Duk da yanayin abin da ya faru, da Abdul sakaci da tarbiyyarsa ne, amma za a iya kamanta rahama da jauhar, Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya ce ka yi sanadin shiriyar mutum ɗaya, ya fi a baka jajayen raƙuma guda ɗari. Ba mu san me Allah ya ɓoye a lamarin nan ba, ga juna biyu a tare da ita, ku na nan ta yi masa alƙawarin ya je ya gama prison ya dawo ta na jiransa. Duk wannan abun fa zai iya yiwuwa wata jarrabawar ce daga Allah muma yake yi mana, Abdul fa bawansa ne shi ma, kuma ya na kishin abin sa, ci gaba da jansa dan Allah ya ara mana dama ba zai haifar da ɗa mai ido ba. Amma ina mai neman afuwar ku, ba ina nufin shari'ar Abdul ta sha ruwa ba ne, sam sonake ayi tunanin mafita. Yallaɓai Al'amin, Allah ya baka haƙuri ni babu wanda ya bani wani cin hanci, ba kuma ƙoƙarin cin amanarka nake yi ba. Zan yi iya yi na Abdul zai je prison in sha Allah, muddin hakan zai samar muku da nutsuwa" ta ƙarasa maganar a nutse, ta ja da baya ta fice. Ramma ta na tsaye ta na ji, gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi, ta fashe da kuka, ganin yadda ta ja aka ɓatawa Nabila rai. Sojan da yake ba wa Nabila kariya, ya bi ta ya na yi mata magana, amma ta share shi, a ranta ta ce "Tsohon munafiki kawai" Napep ta tara, ta nufi gidan Abba. Maman ramma na shirin yin magana, Viper ya rigata, ya ce bari ya tafi. A ɗaki ta iske ramma, ta yi mata ta tas, ta ce "Ramma ba kya tausayina, ɗa na ya rasa ransa a banza, a gabanki yaron nan saboda rashin tarbiyya, ni kaina so yayi da ya haike mini, amma yanzu kin fifita shi a kaina, na gode rahama" Tabbas da zuciya za ta yi mata adalci, to da ba ta fara ƙaunar Abdul ba, amma ita haryanzu ta fi yarda tausayin sa take ji, ya ake so ta yi da rayuwarta ne. Viper na fita, sojan ya fara gaya masa tafiya ta yi, ya ce ya rabu da ita, su tafi kawai. Da daddare Viper ya din ga kiran wayar Nabila, amma ta ƙi ɗagawa, hakan ya tabattar masa da ta yi fushi ne. Gidan major babu wanda ya kulata, babu wanda ta kula sai baba uwani, ta shirya ta tafi gidansu sumayya, sun daɗe su na tattaunawa, ta na yi mata nasiha da ba ta ƙwarin gwiwa. **** Monday morning 9:30a.m Tsaye take a gefen wani gini, tana ƙarewa harabar kotun kallo. Yadda aka cika harabar da manya da ƙananan motoci ne, ya sake tabattar mata da manyan shari'oi za a gudanar a yau. Ta din ga kallon agogon hannunta, tana kallon gate ɗin shigowa harabar kotun. Motar gidan yari ce ta shigo, aka yi parking ɗin ta, sai dai tsayuwar motar babu daɗewa wata danƙareriyar motar, ta shigo harabar kotun. A ƙalla an kai mintuna goma da parking ɗin motar, sannan aka buɗe bayan motar, wata mata ta fito, sanye cikin coat. Mutanen da ke harabar wurin, suka nufeta, wasu suka karɓi jakarta, ana ta yi mata fadanci, cikin girmamawa. "Ya Allah kai ne Allah, kai ne buwayi gagara misali, Ubangiji da babu wani kafinsa, kuma babu wani a bayansa. Allah na san mutanen nan sun fi ƙarfina ta ko ina, amma kai ne abun dogarona, na san ba za ka bani kunya ba. Allah sun fi ƙarfina ka fi mini ƙarfinsu. Allah ka yi mini kunfayakununka a kan shari'ar nan, hasken gaskiya ya shafe duhun ƙarya, duk da ina da masu goya mini baya, amma Allah goyon bayanka nake buƙata" ta jima a tsaye tana karanto addu'a, tare da yi wa Allah kirari. A hankali ta furta "What a hectic trial, Ubangiji ka iya mini" cikin nutsuwa, ta fara taka takalminta mai tudu, ta nufi shiga cikin kotun, da takunta mai kama da na ƙasaita, shigarta ta lawyoyi tayi matuƙar yi mata kyau, tana tunkarar ƙofar shiga, zuciyarta na tsananta bugawa,tana fatan Allah ya shiga lamarin ta. Ayshercool 08081012143 91 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Sannu a hankali ta ke ƙoƙarin shiga cikin kotun, "Nabila" ta jiyo muryar sumayya a bayanta. Ta waiwaya, sumayya ta ƙaraso ta ce "Ya aka yi ki ka riga ni zuwa?" "Oho miki dai" Sumayya ta yi murmushi ta ce "Best of luck my dear, Allah ya ba da sa'a" Nabila ta ce "Amin sumayya, amma a tsorace nake, wannan shi ne trial mafi haɗari da nake tunanin zan fuskanta a rayuwata" Sumayya ta ce "Haba mutuniyar, tsoro ba naki ba ne ba, ke jaruma ce i trust you dear, mu je kawai" Su ka ƙarasa su ka shiga cikin kotun. Su na nan zaune, Alhaji mu'azzam ya shigo, barrister Habib ma ya ƙaraso, sai ga murtala, su liti da Walid, cikin mamaki sai ga Nasir ma duk a cikin kotun daga baya sai ga mai gayya mai aikin shi ma ya iso kotun. Ƙirjin Nabila na ta bugawa, amma ta tsananta maimaita "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, la haula wala ƙuwwata illa billah" Ana ta gabatar da shari'oi, aka kira ƙarar su Nabila. Tashi ta yi cikin nutsuwa, ta fita gaban shari'a. Ta tsaya ta gabatar da kanta a da cikakken sunanta, da kuma wanda take karewa. Lauyan da yake kare lakwari, ya fito ya gabatar da kansa, da wanda yake karewa. Nabila ta nemi a karantowa masu laifi, laifin da ake tuhumar su da shi, a nan ɗan sanda mai gabatar da ƙara, ya karantowa lakwari laifin da ake tuhumar sa da shi, da Madaki, duk da madaki ya na gadon asibiti ya na jinya. Aka karanto tuhumar da turanci, cewar ana zarginsu da shiga cikin gidan Aminu Viper, su ka kashe mata da ɗan da kuma ɗan yake cikinta. Kotu ta waiwayi lakwari domin jin ta bakinsa, bayan an fassara masa ƙusnhin tuhumar da ake yi masa, cikin harshen hausa. A nan take lakwari ya musanta zargin, kamar yadda ya musanta a wurin 'yan sanda, da kuma yadda lauyansa ya jaddada masa kafin zuwan su kotu, domin kuwa ba ƙaramin kuɗi aka ba wa lauyoyi ba, a kan su yi duk mai yiwuwa ayi ta jan Shari'ar har ta lalace. Daga haka kotu ta ɗaga cigaba da shari'ar, zuwa sati biyu domin bayyanar shaidun kowanne bangare. Viper daga in da yake zaune, lakwari kawai yake kallo, ko ƙiftawa ba ya yi, zuciyarsa na raya masa kawai ya kashe shi ya huta, yanzu da haka za ayi ta jan ƙafa a shari'ar nan a ɗauki dogon lokaci ba a kammalata ba? Zuciyar sa azalzalarsa kawai take yi, ya na jin tamkar ba zai iya jira ba. Ya na kallon lakwari, taswirar abin da ya faru a daren da jauhar ta mutu, na ƙara dawo masa a cikin ƙwaƙwalwarsa, yadda ya kasa kataɓus, ya na ji ya na kallonta ta na miƙo masa hannu. Knasa ne ya yi wata irin sarawa, ya tashi cikin hanzari ya fita daga cikin kotun, gaba ɗaya fuskarsa ta sauya, tsantsar baƙin ciki da ɓacin rai, haɗi da tashin hankali ya mamaye ilahirin fuskarsa, tuni idanunsa su ka kaɗa su ka yi jawurrr. Nabila ta na daga in da take ta bishi da kallo, ta san a rina, wani irin tausayin sa ya kamata, kamar ta tashi ta bishi, sai kuma ta tuna fushi take yi da shi, dan haka kawai ta basar. Walid ne ya tashi ya rufa masa baya, liti ma biyo su yayi. Walid ya cimma sa cikin hanzari, ya na kiran sunansa. Bai tsaya ba, Walid ya riƙe rigarsa ta baya, ya juyo ya ture shi, amma ya sake riƙe shi. "Mai laya" ya furta muryarsa na rawa. Walid ya ce "Mai zamani" "Idan zuwana wurin Shari'ar nan zai din ga fama mini gyambon da yake cin zuciyata ina ga zan haƙura kawai" Walid ya ce "Ba zamu haƙura ba, bakin rai bakin fama, sai in da ƙarfinmu ya ƙare da yardar Allah" Wata baranda Viper ya samu, ya zauna, ya miƙe ƙafafuwan sa, ya na jin yadda kansa yake ci ga ba da sarawa bugun zuciyar sa na ƙaruwa. Liti ya zauna a kusa da shi, ya dafa kafaɗarsa ya ce "Haba maza, zuwa yanzu yakamata ace fa ka saba da jurewa, ka yi haƙuri" Viper ya kalli liti ya ce "A ganinka ragwancina ya yi yawa ko? Ba ka san me nake ji ba, yau da jauhar mutuwa kawai tayi Allah ya karɓi rayuwarta, zan yi mata addu'a na haƙura na dangana, sai dai zan rayu da begenta a raina. Abdullahi a kan idona fa aka kasheta, ban iya aikata komai ba, a kan cikinta na watanni tara ta faɗi, ta na kiran sunana, ba ta ji ba ba ta gani ba fa" Viper ya yi maganar cikin ƙunar rai, ya na sauke numfashi. "Mun sani mai zamani, amma ka ƙarfafi gwkwarka, ko ita ma ta samu ta yi abin da ya dace". Ya sauke numfashi ya ce "Wannan karon, muddin aka kuma yi mini abin da aka yi mini a baya, zan ɗauki matakin da nake ganin ya dace" Nabila su ka fito tare da Sumayya, Sumayya cikin damuwa ta ce "To a haka za ayi shari'ar, yau ai ba a yi komai ba" "Ba a yi wa shari'a gaggawa, mace ce mai ciki ba a san me za ta haifa ba, a sannu a ke bi, ba aikin jarida ba ne ba, jakadun yaɗa gulama kwando kwando" Duka wasa sumayya ta kai mata, a lokacin da barrister Habib ya fito, tare da Alhaji mu'zzam su na magana. Viper ya na cikin mota, ya na jiran Nabila su tafi, kawai ta shiga motar barrister Habib, tare da Sumayya. Bai ce uffan ba, ya yi umarnin a ja motar su tafi. Gidan da su ramma su ke, su ka je, Nabila ta ɗauki ramma ta ce za ta fara zuwa awo, maman ramma na matuƙar jin nauyin Nabila, dan haka ta ƙyaleta da ita. Hatta likitan da zai yi mata awon, Abdul ne ya gaya musu wanda zai yi mata, dan kar a cutar da ita. Asibitin abokinsa ne, su na ta hira da sumaya, ramma ko uffan ba ta iya cewa, hankalinta kacokan ya na kan ya jikin Abdul, dan baban fatanta bai wuce yau ma Nabila ta kaita wurinsa ba. Su na shiga wurin likitan, ta ga ya zuba mata ido, ko ƙiftawa ba ya yi. Nabila haushi ya kamata, ta ce "Lafiya kuwa?" Ya ce "Ahh lafiya ƙalau, wani cikin ki ka samu kenan?" "Ban gane ba, matar abokin ka mu ka kawo, Abdul yasar da ya ce kai za ka yi mata awo" Ya ce "Ok Allah sarki, Abdul yasar, ai ya haɗu da larura shi ma, gashi wai ba a zuwa dubiyarsa, ai mun yi mamaki yadda aka yi ya yi aure babu labari" yayi maganar cikin kame-kame ya na kallon Nabila. Ganin ta haɗe rai, ya sanya ya ce "Wacece matar ta sa a cikin ku?" Yayi maganar yana kallon ta ita da sumayya. Nabila ta nuna masa ramma, ya waro ido, Ganin ƙaramar yarinya, bai matsa da tambaya ba, ya ɗauki details ɗin ramma, ya tura su gwaje-gwaje. Bayan sun dawo ya dudduba ya ce "Ya aka yi matar likita take fama da ƙarancin jini har haka, kuma ga shi ta ce ba ta iya bacci, menene yake damunta haka?" Ya tattara hankali a kanta ya ce "Menene yake damunki ba kya iya bacci? Ko dan doctor ba shi da lafiya ne? Ki yi haƙuri zai warware, in sha Allah. Amma dan Allah ki din ga cin abinci yadda yakamata, ki sha magungunan ki, dan kanki ya daina ciwo, kuma ki din ga isashshen bacci, idan ba haka ba, jininki zai hau ki yi jijjiga ƙwaƙwalwarki ta taɓu" Ramma ta jinjina masa kai, yayi counseling ɗin ta sosai, Su ka yi masa godiya, har sun miƙe, ya ce "Baiwar Allah dan Allah yi haƙuri, wai ba Zahra ba ce ba matar Al'amin, da yake ce miki 'yar madara? An ce ya kashe ki, ranar da ku ka zo nan, na ce washegari za ayi inducing ɗinki, kuma yanzu na ganki a raye" Nabila ta yi masa wani marayan murmushi ta ce "Ba ni ba ce ba" "Yaya za ki ce mini ba ke ba ce ba? Ki na ce master fa, ya na ce miki 'yar madara. Idan za ku zo awo, har da abokansa, wani Walid da wanenen na manta sunan su, ranar har ki ke cewa ya goya ki ba zaki iya tafiya ba kin gaji. Na yi miki scanic ya ce na gaya masa da wa ɗan yake kama ke ko shi? Baki gane ni ba, doctor muktar ne fa. A tsohon asibitina fa na gadon ƙaya da ku ke zuwa". Nabila ta yi murmushi, hawayen idanunta ya gangaro. Ta ce "Ka taɓa ganin wanda ya mutu ya dawo? Twin sister na ce, ba ni ba ce ba" sai kuma ya yi shiru ya na kallonta, ya ce "Ikon Allah, Amma ban taɓa ganin identical twins da kamaninsu ya ɓaci fiye da kima ba kamar ku, amma ban taɓa sanin ta na da twin sister ba, mu na hira da su sosai. Duk da mijinta ba shi da fara'a, amma muddin yaga na ba ta kulawa ta musamman sai ya saki jiki da ni ya yi ta mutunta mini. Haryanzu ina mamakin yadda aka yi ya kashe ta duk da irin soyyayar nan da yake yi mata, kamar ya haɗiyeta. Ga ta da sanyin hali, komai ta ce master yarinya mai haƙuri da girmama mutane" Nabila ta katse shi, ta hanyar cewa "Bari mu je doctor, mun gode sosai da sosai". Sai dai su na fita, ta saka musu kuka, Sumayya ta ce "Haba Nabila menene haka? Ya da kuka kuma" "Wallahi sumayya duk lokacin da na tuna ban taɓa ganin jauhar ba, wallahi sabon baƙin ciki nake shiga, sai dai ina jin daɗin duk wanda na haɗu da shi, halinta na kirki yake gaya mini" Ramma ta ce "Ki yi haƙuri ki daina kuka, mu yi mata addu'a, mama na yawan gaya mini, lokacin yaya Nura ya na da rai, kullum ya je sai ya bata labarinta, har ta na ce masa ya samo mata, za ta saka Yaya Aminu ya yi masa aure. Ana faɗar kyawawan halayenta, kamar dai yadda ki ke kema" Duk da kuka Nabila take yi ta ce "Haba, dan Allah nima ina da kirki rahama? Za a iya faɗar alkhairina idan bana raye nima, ba za a din ga cewa masifaffiya ce ni ba?" Ramma ta jinjina kai ta ce "Ki na da kirki sosai Anty Nabila, daga ke har Anty sumayya" "Viper fa?" Shiru ramma ta yi ta na kallonta. A tare Nabila da sumayya suka hau dariya, Ramma ma ta ɗan biye musu ta murmusa. Nabila ta ce "Kar ki ƙullace shi, shi ma mutumin kirki ne, zuma ne kawai sai da wuta, ki yi ta banka masa addu'a, zamu shawo kansa in sha Allah. *** Viper ya na kwance ya na ta juyi a kan katifa, ba kalar rarrashi da ban bakin da su Walid ba su yi masa ba, amma yayi shiru bai kula su ba. Ga wani malulun takaici da ya ƙule shi, Tun bayan da ya shiga iftila'in rashin Jauhar, babu wanda yake jin rarrashin sa ya na ratsa shi, kamar Nabila, gashi saboda wulaƙanci, ta na kallonsa, ya na kallonta, amma tayi banza da shi, ta hau motar da ake fita da ita saboda tsaron lafiyarta amma ta yi burus, duk da ta na kallonsa a ciki, kuma ta san ita suke jira. Jin takaici ya cika masa zuciya, ya sanya ya tashi ya kunna sigari, ya koma gefe ya na ta busa hayaƙi a nutse, sai dai sam ya kasa samun sassauci a ransa. Ya lumshe idanunsa, ya na hango jauhar. Ta kalle shi, yadda ya zuba mata ido, ta na yi wa wani mayafi aikin bead. "Mazajena ya aka yi ne?" Guntun tsaki ya ja ya na daga kan doguwar kujera ya ce "Gaskiya na gaji, haba ke baki san me nake ji ba ne ba, wallahi kara uku na sigari ɗaya safe ɗaya rana da dare kamar wani magani, gaskiya yayi mini kaɗan, gaba ɗaya kin takura mini rayuwa kin hanani sukuni haka ake yi, ba sai ki bari na je na sha a waje ba, idan ma ba kya so na sha a gabanki ne ba" yayi maganar yana jin haushin kansa, yadda ta kirshe shi a gida, kamar wani ɗan ta wai ba zai fita ba, hadda ƙayyade masa iya adadin abin da zai sha" Murmushi ta sakar masa, duk da faɗa yake yi, gashi dai ba ɗaure shi ta yi ba, amma ya na zaune ya na masifa, saboda ya san ya na fita ranar ba tausa ba hira, ba zata saurare shi ba sai ta wana shi. Ta ƙarasa gaban kujerar ta na masa murmushi, ta na kallon yadda ya wani maze ya na kumbura, ba kuma iya rashin shan sigarin ne ya sanya yake ta faɗa babu gaira babu dalili ba, period take yi shi ne abin da ya ƙara sanya shi faɗan, yake cika ya na batsewa. Ta shafi sumarsa ta na murmushi ta ce "Manya gatan wasa, tuba nake yi, kaina bisa wuyana, ban yi hakan dan takura walwalarka da nishaɗinka ba, lafiyarka nake yi wa. Ayi mini afuwa a daure a lallaɓa da kara ukun nan, zan soya maka wainar fulawa mai ɗan karen daɗi, fanka kuwa sai ka kasheta dan kanka, panel ɗin ya samu isasshen hasken rana, ba zaka kwana cikin zafi ba, za ka samu wadatacciyar iska, a maimakon sigarinka da na hanaka, ai ka na so ko?" Tunstirewa ya yi dariya ba tare da ya shirya ba, ya janyota jikinsa ya ce "Wai ke mai wayo ko?" Ita ma dariyar ta yi ta ce "Ai na san ba faɗan sigarin kawai ka ke yi ba, tari idan ka yi master na san me ka ke nufi" "Aishikenan, ɗaukko abin mayafin da na tayaki, ko kuma wani abun zan yi miki" Ta ce "Inyee duk murnar fankar ce za a tayani aikin bead ɗin da ake watsar mini" Ya ce "To kin yi wa kanki, na fasa tayakin" "Bakomai zauna ka ci gaba da kallona, hakan ma ya wadatar da ni ɗan aljanna na" Murmushi ne ya suɓuce wa Viper, lokaci guda ya na haɗiye hawayen da suke ƙoƙarin zubo masa. Ya saki sauran sigarin hannunsa, ya na sauke numfashi a hankali. "Allah ban san dalilin da ya sanya ka karɓi jauhar, ka shigo da Nabila rayuwata ba, amma duk abin da ka yi dai-dai ne. Astagfirullah wa atubuilaihi Allah ya yi miki rahama ya sada ki da annabin rahama matata" *** Gidan su Nabila kuwa tun da Nabila ta zo, aka yi wannan fashe-fashen, tonon sililin, gidan ya ƙara rikicewa, Zakiyya kamar ta tsine wa Hafsa faɗar abubuwan nan da ta yi. Faɗa da tashin hankali ya ƙara kacame wa a gidan, Baba kuma ya ƙaurace musu gaba ɗaya, ya daina shiga shirginsu, ya daina cin abincin su, ya din ga kaɗaice kansa daga shiga cikin su. Wata irin sabuwar damuwa ta addabe shi, dana sani ta aure shi, ya din ga jin tamkar ya mayar da hannun agogo baya ya gyara wasu abubuwan da su ka shuɗe. Gaba ɗaya nauyin Nabila yake ji, gashi tun da ta tafi, ba ta sake waiwayarsa ba, gashi ya na matuƙar son ganinta, amma babu hali dan nauyinta yake ji, dan a zatonsa fushi ma take yi da shi. Gashi kamar yadda ta faɗa lallai akwai buƙatar samun daidaito a tsakaninsa da major. *** Nabila ta gaji da yawa, kai tsaye gidan major ta wuce, ta saka mukulli ta buɗe ɗakinta, babu wanda ya kulata sai baba magajiya, tare su ka yi ta hirarsu, ta na ba ta labarin yadda shari'a ta kasance a falo. Mama sai hararta take yi, tamkar idanunta, za su faɗi Nabila ko a jikinta. Unexpected Nasir ya shigo ya tarar da ita a falo, duk ta rame sosai da sosai. Kamar ya shareta ya wuce, sai kuma ya kasa, ya ce "Ashe an fara shari'ar?" Kamar ba za ta yi magana ba, sai kuma ta numfasa ta ce "Ai ba ashe ba ne DSP, tin da ka halarci shari'ar kai ma" Ya yi murmushi ya ce "Haka ne, to ayi dai mu gani" "In sha Allah za ku ga alkhairi, muddin da jinin major Yusuf maitama a jikina, zan ci gaba da tsayawa a kan gaskiya, kuma zan yi nasara in sha Allah" ya kalleta ta basar ba ta kuma magana ba. Nabila na ta son ta kira Viper, ta ji yaya yake, kuma ta bashi labarin likitan nan, amma ta basar da ta tuna da maganganun da ya caɓa mata. Washegari da wuri ya tafi gidan madam Halima ya na muzurai, a zatonsa Nabila ta na can, amma madam ta ce "Ba ta dawo ba fa tun jiya, Nabila ta na wasa da rayuwarta, ba ta san a iya haɗarin da take ciki ba, an ba ta security amma abin da ta ga dama take yi" Viper ya gyaɗa kai ya ce "Zan yi mata magana" Ya duba wayarsa, ya duba location ɗin ta, ya ga ta na gidan Major. Nabila kuwa da safe da ta shirya, ta je ta samu Abba ta gaishe shi, ya amsa mata sama-sama ta tashi ta fita. Ƙarfe sha ɗaya na safe, ta na asibitin da Abdul yake kwance. Cikin sa'a mahaifiyarsa ta na nan, ta na ganin Nabila ta tsuke fuska, ta na tambayarta uban me ya kawo ta. Abdul ya ce "Mummy ki tsaya mu je menene mana?" "Ba za a ji ɗin ba, uban me za ta zo da shi na alkhairi wannan" Nabila ta numfasa ta ce "Magana ce mai muhimmanci na zo zan yi da kai" Ya kalli Mummy ya ce "Dan Allah ki yi haƙuri, ki bari mu yi maganar nan, bamu san ta zo da shi ba" tashi ta yi ta fice ta na tsaki. Nabila ta ja kujera ta zauna, ta kalleshi ta ce "Ya jiki kuma?" Ya amsa da "Alhamdilillah" "Na biya wurin likita, ya ce ana samun improvement a ciwon naka, yanzu kuma damuwa ce ka saka a ranka tayi maka yawa. Ɓangaren rahama ma, na kaita awo wurin likitan da ka ce, a kaita" Cikin sauri ya ce "Komai lafiya ko?" "Ba na ce ba, tun da ta yi complain da cewar ba ta iya bacci, ga ciwon kai, jininta ya yi ƙasa saboda ba ta cin abinci" Cikin damuwa ya ce "To meyasa?" Nabila ta ce "Abu ɗaya ke damunku kai da ita, sai dai kafin mu zo nan, mu fara tattaunawa a kan tubalin dalilan matsalolin da suka yi wa muradinku ƙawanya. Zan fara da yi maka tambayoyi ka bani amsa, ta haka ne kawai za mu kamo bakin zaren. Zamu yi magana ne a matsayin mutum da mutum, ba wai a matsayin lauya da mai laifi ba" Ya jinjina kai ya ce "Ina jinki" "Na san ka na cike da jin takaicin yadda Viper ya ƙara dagewa kai da fata, a kan lallai a hukuntaka, amma ka san Viper kafin yanzu?" Ya gyaɗa kai ya ce "Na san shi, yaron mahaifina ne" Nabila ta ce "Wane irin aiki yake yi masa?" Ya ɗan yi jimm sannan ya ce "Abin da ya shafi harkar daba ne" Ta ce "Good, meyasa kai ba ka yi masa, duk da na san ka fi Viper morar mahaifinka, kai ya kai ka waje ka yi karatu shi kuma ya bashi ƙwaya da makami, ya bar shi a sake a cikin al'umma? Ko kuma shi ba shi da ƙwaƙwalwar dai idan an biya masa kuɗin karatu, ba zai iya ba?" Abdul ya yi shiru. "Mahaifinka ya yi wa Viper laifukan da su su ka zama kanwa uwar gamin ruruta wutar ƙiyayyar da yake yi wa mahaifinka ce ta gangaro zuwa kanka. Na san ka san meyafaru da Nura guduma zuwa yanzu, duk da ba abu ne mai daɗin da zan ta nanata shi ba, hakazalika ban sani ba ko ka san abin da mahaifinka ya yi wa Viper. A kan case ɗin Nura ya aika a kashe Viper, amma aka ɓuge da kashe matarsa, wadda take twin sister ɗina, kuma aka rufe shi shekara biyar da zargin shi ne ya kasheta" cikin tashin hankali da mamaki yake bin Nabila da kallo. "Ta yaya ka ke tunanin Viper zai iya yafe wannan tozarci da aka yi masa, Ramma ƙanwace a wurinsa, ya na da dangantaka da ita ta ɓangaren uwa, shikaɗai ne yake tsaye a kansu, yake taimaka musu. Ya na ɗora alhakin mutuwar Nura a kansa, dan haka ya na jin dole yayi duk mai yiwuwa ya yi supporting ɗin su. Ni ya damƙawa ragamar shari'ar rahama, kamar yadda ragamar ta sa shari'ar ma take hannuna. Da zafina har cikin zuciyata nake son na ga an hukuntaka, saboda abin da ka aikata ya tsaye mini. Ga rape, ga tozarta uwar yarinya, ka sace mata 'ya, ka yi amfani da dukiya wurin aurenta ta ƙarfin tsiya. Aka kama wani daban aka ɗora masa laifin, ƙarshe ma aka kashe shi, duk dan a kare ka. Banda waccan azzalumar matar mai rufe kura da fatar akuya da take zaluntar mutane, Naja bunkure wadda na yi wa kaina alƙawarin tona mata asiri. Sai dai abin da na gani ya bani mamaki, daga gareka da kuma rahama, na bibiyi wasu abubuwan da su ka faru babu saka hannunka. Amma dagiyar da muke yi, kowa da gaskiyar sa, twins sister na ban taɓa ganinta ba, duk da wani labari ne daban, amma ko ba komai, na shigo cikin labarin nima. Yanzu abin da nake so da kai, gaskiya ni na karaya, ka tattauna da lauyoyinka, mu yi zama na musamman a kai mu shari'a law, saboda ka samu sassauci ko yaya a hukunta ka dai hankalinsu ya kwanta, ina tunanin makomar Rahama da abin da yake cikinta, they really need you. Ka cire girman kai da duk wani abu, ka roƙi alfarmar Viper da mahaifiyar rahama, ita dan ta rahama a ƙyaleka ba sai an hukuntaka ba. Ta na ta yi mini magiyar a sassauta maka. Amma ya ka gani" Abdul ya ɗan yi shiru, ƙarshen ƙasƙanci dai ace ya durƙusawa Viper, yaron mahaifinsa da ba sa ga maciji ƙasƙantaccen ɗan daba, amma ba shi da wani zaɓi sama da hakan. Ya numfasa ya ce "Na amince da hakan" Ta ce "To Alhamdilillah, ba amincewarka ba kawai, ka tattauna da lauyoyinka. Ni kuma zan san yadda zan shawo kansa, a yi zaman tattaunawar ka san murɗaɗen mutum ne, da ba ya sarrafuwa cikin sauƙi, amma dai ka yi shawara" Ya amsa da "Shikenan, na gode sosai da sosai, da ƙoƙarin da ki ke yi mana, dan Allah ki gaida mini da rahama, ki ce na ce dan Allah ta kula mini da lafiyar su, ta daure ta din ga cin abinci " Nabila ta yi murmushi ta ce "In sha Allah" *** Aka shafe sati guda, Nabila da Viper ba su haɗu ba, ta koma gidan major ta yi zamanta, mutanen gidan babu mai iya tanka mata. Viper ya sha mamakin yadda Nabila ta watsar da shi gaba ɗaya, idan ya ɗaga waya kamar ya kirata sai ya fasa ya ga kamar ya faɗo. Ita kanta daurewa kawai take yi, ba ƙaramin azalzalarta zuciyarta take yi, a kan ta kira Viper ba, ko ta je in da yake ba, amma ta dake. Lauyan Abdul ya kira Nabila a waya, ya sanar mata da sun amince ayi zaman sulhun. Nabila ta na zaune a office ɗin ta, ta na tunanin yadda za ta shawo kan Viper a kan lamarin ramma. Ta cire kayan jacket ɗin ta, daga ita sak dogon wando da shirt, ta ɗora ƙafafuwanta a kan tebur, ta ajiye popcorn a wata container, ta na ci kaɗan kaɗan ta na tunani. Buɗe ƙofar ya yi ya shigo, tare da yin sallama ƙasa-ƙasa. Ita ma a cikin ta amsa masa, ta ɗauke idanunta daga kansa, ta maze. Har ya ƙarasa gaban teburinta, ba ta motsa ba. Ya daddaki teburin, ta ɗago, ya kalli ƙafafuwanta ya kalleta. So ta yi tayi burus da shi, sai dai ya yi mata kwarjini, ta sauke ƙafafuwanta, ta na yamutsa fuska. Ya matso kanta ya tsaya, ya yi gyaran murya ya ce "Kin koma asibiti wurin yaron indabo, me ki ka je yi? Next week idan Allah ya kaimu cigaban shari'ata, ya ake ciki?" Ta kalleshi ta ce "Ya ka ke bibiyata kamar wata ɓarauniya ne? Na je wurin Abdul, za mu sake zama da su na musamman, kafin mu shiga kotu. Shri'arka kuma normal ne, ban karɓi cin hanci daga wurin kowa ba, na tanadi duk abin da yakamata". Sarai ya gane magana take gaya masa, da take nuni da abin da ya sanya ta fushi, amma ya basar ya ce "Zaman me kuma za a kuma yi a kan shari'ar ta, ba kotu kawai za a kai mu ba, me ake jira ko wani abin dai ki ke kuma shiryawa ban sani ba. Sannan ki na kasada da rayuwarki yadda ki ka ga dama, ba ki san ta ina za a iya kawo miki hari ba amma ki na yawo yadda ku ka ga dama a gari" Tashi ta yi tsaye ta ce "Allah zai kare ni, ramma kuma idan ka na kokwanto a kai na, ka canza mata lauya, ka daina zargina babu dalili, ka na yi mini masifa" tayi maganar ta na nufar hanyar fita. Kamar ya riƙo kyanwa, ya janyo ta ta baya, ta dawo gabansa su na fuskantar juna. Hakan ya bata damar shaƙar warin sigarin da yake yi, wanda daga nesa ba aji, saboda turaren da ya saka. Ya ɗago mata jacket ɗin ta, da take shirin fita babu ita, ya na ci gaba da tsareta da idanunsa. Da idonsa kawai ta gane meyake nufi, amma in da yake kallo a jikin nata ya ƙara razanata, jikinta ya hau rawa. Ya ɗora mata rigar a kafaɗarta, ya ja da baya, wata irin kunya ta mamayeta, dan kai tsaye ƙirjinta ya zuba wa ido. Da ƙyar ta aro jarumtar da ta ce "Vi wiwi ka sha ko?" Ya waiwayo ya tsura mata ido, ta ɗauke kanta ta ce "Kar ka mayar mana da aiki baya" Ta yi maganar ta na ƙoƙarin buɗe ƙofar office ɗin ta fita hannunta riƙe da rigar. "Idan ki ka fita ba ki rufe jikinki ba, ranki zai yi mummunan ɓaci". Ta waiwayo ta ce "Malam know your limit, ka daina ba ni umarni yadda ka ke so" tayi maganar tana hararsa. Ayshercool 08081012143 92 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Ba ƙaramin haushi ne ya kama Viper ba, ba fitsarar da Nabila ta yi masa ce ta baƙanta masa rai ba, yadda ya kasa sarrafa kansa, har ya shagala da kallon abin da ba halalinsa ba ne ya fi komai ɓata masa rai. Sai dai wani irin matsanancin kishi ya taso mata, ganin da gaske a hakan ta fita, bin hanyar ya yi ya fita, ya tarar da ita a reception ta saka rigar, su na magana da Barrister Habib. Barrister Habib ya na ganinsa ya yi murmushi ya ce "Yau ziyara ka kawo mana, barka da wannan lokaci" yayi maganar yana miƙa masa hannu. Nabila ba ta saka ran zai kula Barrister Habib ba, amma ta ga ya miƙa masa hannu, su ka gaisa Viper ya bi hanyar fita ya fice. Nabila kuwa murmushi ta yi, ganin yadda ta kunna shi, ko ba komai ita ma ta rama. **** Alhaji mu'azzam tun da ya sake haɗuwa da hafsa bayan rabuwar su, kawai ya ji ya na matuƙar jin tausayinta, har ga Allah ya na son Nabila ma, sai dai ya san Viper ba zai taɓa barin sa ya aureta ba, ko da zai samu aurenta sai an kai ruwa rana, amma matuƙa tausayin hafsa yake ji. Ya na ta bibiyar unguwar ko zai samu ya ganta. Ranar da ya sake zuwa wurin Baba kuwa, Allah ya taimake shi, ya ganta ta dawo daga islamiyya, dan kuwa islamiyya ta koma, idan ta je makaranta ta na samun sassauci daga damuwar da take damunta. "Baba na dawo" "Sannu da zuwa" Baba yayi maganar ya na kallonta. Ta saka kai za ta wuce, duk da yadda Alhaji mu'azzam yake ta kallonta. Baba ya ce "Hafsatu ba ki ganni da baƙo ba ne?" "Na ganshi" "To ba zaki gaishe shi ba?" Ta kalleshi ta zumɓura baki ta ce "Ina kwana?" Baba ya ce "Kwana kuma da yammacin nan?" Alhaji mu'azzam ya ce "Hakan ma na gode, lafiya ƙalau ya makaranta?" Ba ta amsa ba ta shiga cikin gidan. Ya na so ya yi wa baba maganar hafsa, mussaman da ya samu labarin, ta samu matsalar ƙwaƙwalwa, amma ya kasa. Bayan baba ya shiga gida ya hau ta da faɗan abin da ta yi kawai ta fashe masa da kuka ta ce "Baba ni ko son ganinsa ba na yi ne, amma ai na gaishe shi, ni na tsane shi ne" Baba ya waro ido ya ce "Hafsatu, ba a cewa an tsani mutum, ko ba komai auratayya ta taɓa haɗaku, ba ki san mai zai faru gaba ba, ki daina haka" But Zakiyya ta fito ta ce "Baban saifu, Alhaji mu'azzam ɗin ne ya zo, ko bikonta ya zo yi?" Hararta Baba ya yi, kawai ya wuce turakarsa, daga ita har Babbar su saifu ya watsar da su, ko turakarsa su ka je korarsu yake yi. Da yaransa kawai yake harkokinsa, shi ma kuma ba dukkansu ba, saifu ne sai Hafsa, mussaman hafsa da yake jin tausayinta. Zakiyya ta saka Hafsa a ɗaki, a kan yadda za su lallaɓa a sasanta ta koma gidan Alhaji mu'azzam, A take ta ce Allah kar ta ko shi ne autan maza ba za ta koma gidansa ba, ita yanzu islamiyya za ta yi ta zuwa, ta zama malama ta din ga yi wa addini hidima har ta mutu. "Wallahi baki isa ba hafsa, ka ji baƙar muguwar yarinya, yi wa addinin hidima ba sai ki yi a ɗakin mijinki ba, wallahi sai kin koma, ba zaki yi mini baƙin ciki ba" "Wallahi ba zan koma na ci gaba da zaman boranci ba, ai tun farko dama ba so na yake yi ba, ki ka saka dole ya aure ni, wallahi ba zan koma ba" Zakiyya ta rasa yadda za ta yi da ranta, ta shirya ta tafi gidan su Viper, wurin ƙawar cin mushenta rahila, dan lambar wayarta ba ya shiga, rabonta da ita, tun ta na Asibiti bayan Abba ya daketa. Sai dai ta tarar da ita cikin damuwa da tashin hankali ita ma, shahida ta kashe aure, Amira an sake gwaji babu HIV sai ciki, ta zubar da cikin ta gudu, ga Abbu ya kori Abba daga gidansa, Naziru kuwa tun da ya tafi kudu ba ta sake ganinsa ba, sai labari da aka kawo mata ya zama riƙaƙƙen ɗan iska a kudun. "Rahila yanzu ina zamu saka ranmu, maigidanmu fa duk ya yi watsi da mu, yanzu ya gano ɗaya yar ta sa hankalinsa ya na kanta, soyake ya lallaɓa ta dawo hannunsa, gashi daga gani ba ta da kunya. Ba na son Alhaji mu'azzam ya san da ita ya ce ita ma so yake yi, hafsa ta kasa komawa ɗakinta, ta ɓangaren ki babu wani zazzafan malamin ne?" "Zakiyya da alama ruwa ya ƙare wa ɗan kada. Dan yanzu asirin ba cin mazajen yake yi ba, har su ma yaran. Gaba ɗaya yarana sun ɗaiɗai ce sun tsiyace babu wani mai ɗan dama-dama sai shahida, Abba ya ɓaci da shaye-shaye tuburan" Zakiyya ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wannan shaye-shayen ya zama bala'i. Ni fa da depression da shaye-shayen ne su ka haɗu su ka saka hafsa hauka" nan su ka ci gaba da jajanta wa juna. *** Da daddare Nabila na shirin kwanciyar, take kallon wayarta, ji take yi tamkar ta kira Viper, dan ta san ta gama ƙular da shi, amma ta dake taƙi kiransa. Washegari da safe ta tura masa message da "Mu haɗu a CID da ƙarfe goma, saura ka ƙi zuwa, wani abin ya biyo baya ka ce an bani cin hanci" Jujjuya wayarsa ya din ga yi ya na kallon saƙon nata. Gaba ɗaya su ka haɗu kusan lokaci guda, daga ita har Viper kamar ba su san juna ba, sai basar da juna suke yi. Babar Abdul sai cika take ta na batsewa, kamar ita aka yi wa laifi, ta na kallon ramma da take ta rufe cikinta kallon banza. Abdul kuwa satar kallon matarsa yake yi, kallo ɗaya ya yi mata ya tabattar da maganar Nabila na ƙarancin jini da kuma damuwa a tattare da Rahama, gashi duk ta rame ga pimples ƙanana sun feso mata saboda ciki. Tausayinta da ƙaunarta su ka mamaye shi, ya ji ina ma su na tare, ya ciyar da ita da ingantattun abinci masu gina jiki, da kulawa ta musamman. Ɗaya daga cikin lauyoyin Abdul ya sake gabatar da kansa sannan ya ce "Mu na godiya da amincewa da ku ka yi ku sake zama da mu, domin a duba a ga abin da zai yiwu na mafita da kuma masalaha a kan wannan case". Mahaifiyar Abdul ta ce "Go direct to the point. Su faɗi ko nawa su ke so, idan ma kuɗin da ya ba su bai ishe su ba, zamu ba su kuɗi, su ƙyale mini ɗa a nema masa lafiya. Dan na gaji da wannan sintirin ba yau babu gobe ana wulaƙanta ni da ni da yarona saboda wata ba ƙauyuyiyar yarinyar" Cikin ƙunar rai babar ramma ta ce "Uwa uwa ce, babu banbanci tsakanin abin da ki ke ji a kan ɗanki da wanda nake ji a kan 'ya ta. Da mazajenku sun sauke hakkin da Allah ya ɗora musu na al'umma, mussaman na karakara da babu yadda za ayi yaranmu su fito birni aikatau dan nema mana abin da zamu rufa wa kanmu asiri, balle yaranku marasa kirki da tarbiyya su keta musu haddi. Da sai dai can su haɗu da watsatsu irin su su lalace, ba dai da yaranmu ba. Ba komai kuɗi zai iya saya ba, an riga an cuceni, ko a hukunta ɗanki ko ba a hukunta ɗanki ba, ya riga ya cuce ni, ubansa ya kashe mini ɗa, ɗanki ya keta wa ya ta haddi, ya dawo ya nemi nima ya keta mini haddi, ya jaddada mini shi ya yi wa 'ya ta fyaɗe na yi abin da zan yi ya ɗauke ta ya tafi da ita. Ubansa kuma ya ci gaba da bibiyar mu da yinƙurin sakawa a kashe ni, dan na nemi hakkin 'ya ta, uwa ce fa ni sukenan yaran uku, uba ya salwanta mini rayuwar ɗa, ɗanki kuma ya kassara rayuwar 'ya ta, kuma ki na gaya mini nawa zaki bani, ki je can da tsiyarki, ɗa ne na ji ɗan sunna ne, za ta haife shi a kawo muku tsiyarku, amma ba zan bar wurin nan ba sai ya sakar mini 'ya" ɗif kowa ya yi yadda maman ramma take kuka mai ƙarfi, wanda yake fallasa asirin zunzurutun baƙin ciki da takaicin da yake cikin zuciyarta. Ramma ta ƙanƙame mama, ta na jin tamkar ba ta yi wa kanta adalci ba, ba ta yi wa mahaifiyarta ba. Nabila ma gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi, a hankali Abdul ya saukko daga kan kujerar da yake, ya je gaban babar ramma ya durƙusa a kan gwiwoyinsa sai dai ya kasa ɗaga kansa, kuma ya kasa magana. A hankali kuma ya ce "Tabbas ahalina sun zama tamkar wata muguwar kibiya, da ta rusa miki dukkanin ginin rayuwarki da ta yaranki. Idan rahama za ta iya tunawa kwanki kaɗan su ka rage na nemeta na rasa, ta farka ta ganni ina kuka cikin dare. Na yi kuka ganin abin da mahaifina ya aikata, abin ya bani tsoro. Sai dai ina neman afuwarku, dan Allah kar a hukunta ni da laifin da babana ya aikata, a hukunta ni da iya wanda na yi, ba zan iya ɗaukar hukuncin laifukansa ba. Dan girman Allah mama ki yi haƙuri, yadda ki ke iƙirarin ke ma uwa ce, ko sau ɗaya ki kalle ni a matsayin ɗanki, idan ya tsinci kansa a halin da nake ciki, ya tuba yayi nadama, watsar da shi za ki yi, ko kuma rungumarsa za ki yi ki ci gaba da yi masa addu'a da fatan shiriya?. Na cutar da ku, kuma na san jarrabawa ce, Allah ya jarabce ni da matsanancin son rahama. Ina nan a kan bakana, a hukunta ni, zan karɓi hukuncin da duk aka yi mini, amma dan Allah kar ku ce na saki rahama wallahi ba zan iya ba. Sannan dan Allah mama kar ki tsani abin da rahama za ta haifa, wallahi ɗan halala ne, kar laifina ya shafe shi, shi ma ya zama lalatacce". Ya kalli in da Viper ya ke ya sunkuyar da kai ya ce "Duk da ina ganinka tare da mahaifina, ban san iya girman alaƙar da take tsakaninku ba, ban san laifukan da ya aikata maka ba, babu sanya hannuna, ban sani ba. Amma duk da haka kai ma ina baka haƙuri, dan Allah kar ka hukunta ni da laifukansa, dan Allah kar ka ce na saki rahama. Ka san me nake ji, tun da ka taɓa tsintar kanka a makamancin halin da nake ciki, ba ƙarya nake yi ba da nake nanata muku, ina son rahama, dan Allah ku daina cewa na rabu da ita, ko in saketa, idan ciwon na bai kashe ni ba, tsana da tsangwamar da ku ke yi mini zai iya halaka ni" "Amma Abdul ka yi asara ka bani kunya, yanzu duk a kan mace ka ke wannan abin? Yanzu halin da mahaifinka yake ciki da ɗan uwanka bai sanya ka yi kuka ka kira wa kanka mutuwa ba sai a kan mace?" "Mummy waye silar shigata wannan halin, laifukan waye su ka ƙara yi wa rayuwata ƙawanya, daddy mahaifina ne, ya yi iya ƙoƙarin sa a kaina, amma laifukan da ya aikata sun shafe kimarsa, babu abin da zan iya yi a kan abin da ya aikata face na yi masa addu'a, kuma ya saduda ya nemi yafiyar waɗanda ya zalunta" Shiru Viper ya yi ya juya ya fice, haushi ne ya kama Nabila, wace irin zuciya da Viper hake ne. Maman ramma ma shirun tayi, ya riƙe hijjabin rahama, cikin marairaicewa ya ce "Dan Allah ki saka baki rahama, ki ce su yafe mini, kar su rabani da ke ba zan iya ba" Ban da uban tsaki, babu abin da take yi. Nabila Viper ta bayan Viper ta biyo ta na mita. "Haba Vi, abin da ka ke yi ba ka kyautawa, haba dan Allah, ai atleast ko ba zaka amince ba ka tofa wani abun ko" shiru ya yi bai yi magana ba, bai kuma waiwayo ba. Nabila ta zagaya, sai ta ga ya na share hawaye da handkerchief, ta fuskanci duk lokacin da za ayi maganar abin da ya shafi jauhar, ƙarara yake karaya, wasu lokutan sai ya zubar da hawaye. A kullum ta na jinjina girman ƙaunar da yake yi mata. "Vi menene kuma? Kukan me ka ke yi" "Leave me" ya faɗa ya na kawar da kansa gefe. "Amma atleast yakamata ka ce wani abu ai" "I say you should leave me, muddin ina kallonsa ina tuna Indabo ne mahaifinsa, ba zan taɓa aminta ayi duk wani abu da zai sanya ya samu sassauci ba. Sai dai ya yi gaskiya na san abin da yake ji, dan har gara shi da ni, ni abin da nake so ɗin ubansa ya yi mini silar rasa shi, ba na fatan ya shiga mawuyacin halin da ni na shiga a silar rashin abin da yake so. Ba kuma zan iya watsa wa mahaifiyar rahama ƙasa a ido ba, dan haka ba zan sake cewa komai ba, abin da mahaufiyarta ta yanke shikenan" Jikin Nabila ya yi sanyi, hakan ya na nufin ya saukko, ya sassauta abin da ya ƙudurta a kan Abdul, sai dai ba kowa zai gane hakan ba, sai wanda ya san shi ya saba zama da shi. A hankali ta koma ofishin, ta tarar still maman ramma ba ta ce komai ba, sai kuka da take ta yi. Nabila ta ce "Ina ga, yakamata a bamu ko 3days ne, mu yanke shawarar ƙarshe" A haka su ka watse, Abdul ya so yayi magana da ramma amma sai haƙura ya yi. Bayan Viper ya koma gida, ya din ga tunani, sosai ya ga tsantsar nadama da damuwa a idon Abdul, wanda da mutane mai izza da jin kansa, ga gayu da hutu, amma shi ne duk ya koma haka saboda soyayya. Ɗan mama kuwa an sako shi, kawai sai ganinsu su ka yi ya dawo, liti ya saka shi a gaba, ya na tambayarsa waye ya sako shi?. Ɗan mama ya ce "Dama ni ai ba laifin komai na yi ba, kawai shaida ne ni dan mugunta aka garƙame ni". "Ɗan mama ka ji tsoron Allah, ko waɗanda ka ke kai wa munafuncin ne su ka karɓo ka" "A'a sakina kawai aka yi" Nabila kuwa Alhaji mu'azzam kankarofi ta kira, ta gaya masa halin da ake ciki a kan lamarin ramma. Ya ce "To ke ya ki ke gani barrister?" "Sonake ka yi wa Viper da maman ramma magana, su yadda aje shari'a court kawai, tun da ya yi nadama, ko dan ɗan da yake cikin ramma" Kankarofi ya ce "Ni a su wa zan yi wa Viper magana, taɓ babar rahaman dai wannan gayen ai sai dai ke ɗin, haka kurum ya din ga yi mini kallon banza ba zai yiwu ba" "Na sani ya na da zafi, amma mutum ne mai sauƙin kai" "A'a ban ga alama ba, ke dai ki ji da shi, zan yi wa mahaifiyar rahama magana" suka yi sallama a kan haka. Alhaji mu'azzam da kansa ya je gida, ya din ga rarrashin maman ramma ya ce "Na san an yi miki laifi, amma yanzu sai mun so za a cigaba da yayata abin da ya sameta. Wasu lokutan sai an jarrabaka ka ke samun ni'ima. Ba dan abin da ya faru ba da babu lallai na sanku, balle na taimaka muku. Da babu lallai garinku su samu albarkacin rahama, ta na son mijinta, idan har ki na son farincikin rahama, ki daure ki yi haƙuri, an san duk wanda aka ce wa ya yi haƙuri an cuce shi ne. Amma abin da zai sanya namiji ya yi wa mace fyaɗe ta dawo ta na sonsa ba ƙarami bane ba, su suka zauna da juna, Allah kaɗai ya san irin zaman da su ka yi ta fara son abin ta. Ki yi haƙuri, ki yi haƙuri ki yafe masa kamar yadda ya nema, yayi nadama na je na ganshi ai, saboda na taimaka muku, matata ƙanwar ubansa yanzu ta bar mini gida, wai na tozarta ɗan uwanta, kuma rahama mai aikinta ce, ba irin bautar da ba ta yi mata ba, kuma ban tsaya muku dan ina son ɗaukar fansa a kan ubansa ba, na tsaya muku ne a matsayina na uba, wanda na haifa nima, ba zan so ayi mini haka ba, amma ki yi haƙuri, ba kuma dole zan yi miki ba ba a yafiya dole, amma ba ki san me Allah zai yi miki ba albarkacin yafiyar ba. Abin alfahari ne a sanadin rahama Allah ya shiryi Abdul" ya daɗe ya na yi mata nasiha mai ratsa zuciya. Ta amince da a kai ƙarar shari'a Court, dan Abdul ya samu sassauci. Amma hakan bai yi wa babar Abdul daɗi ba, a gaban Alƙali aka karantawa Abdul laifinsa, a chamber alƙali a ka yi shari'ar, domin privacy ɗin rahama da identity ɗin shi kansa Abdul ɗin. Ana karanta masa laifin, Abdul ya amsa, Alƙali ya ce a kai masa shi prison, bayan sati uku a dawo ya ci gaba da saurarar ƙarar. Waro ido Rahama ta yi, ta san Abdul ba zai iya zaman prison ba, babu yadda lauyoyin Abdul ba su yi ba, a kan a bayar da belin Abdul, amma Alƙalin nan ya murtuke ya ce babu wannan. Babarsa ta ce "Shi ya janyo wa kansa, dama haɗa baki aka yi, aka zo shari'a court, dan a kulle shi a tozarta shi" Aka taso ƙeyar Abdul, Rahma  ta kasa damuwarta da ruɗewa, ya kalli maman ramma ya risunar da kansa. Ta bakin lauyoyin sa, suka yi wa su Viper godiya, bisa alfarmar da aka yi musu, aka gabatar da shari'ar kotun addinin Muslunci. *** Nabila na office ɗin ta a zaune, Sumayya ta turo ƙofar ta ce "Suprise" Nabila ta ce "Ko ma ki yi mini sallama malama" Sumayya ta ce "Ba zan yi ba" Nabila ta yi murmushi ta ce "Ki ci kanki" Sumayya ta ce "Nabila ana ƙoƙarin hana gudanar da recall election, an kuma sake ɗagawa ba ki ji raina ba" Nabila ta kwaɓe baki ta ce "Mhmm, ai na san a rina, sai dai idan ba a ƙasar nan muke ba, na ji ana maganar EFCC za su sake shi, amma haryanzu babu wani tartibin bayani a kan laifukan da ake tuhumarsa da shi" Sumayya ta ce "Za kuwa mu yi raising alarm a social media, lallai ayi mana bayanin meyake gudana ina kuɗin al'umma suke?" Nabila ta kwashe da dariya ta ce "Ɗansa ya wawushe fiye da rabi, ya yi wa matarsa hidima, Ai Allah ba azzalumin sarki bane, kuma wani ikon Allah yaƙi faɗar ɗansa ne ya wawushi kuɗin" "Ya za ayi ya faɗa, dama fa ware su aka yi dan yayi campaign, shi kuwa yayi campaign a in da ya dace. Wai ina mutuniyar ki Naja'atu Bunkure ne?" "Oho mata na daina jin ɗuriyarta, ina nan ina tattara ƙorafe-ƙorafe a kanta, zan kai ma'aikatar Shari'a, she's not suppose to practice law at all, her licensed must be seazed in sha Allah" Sumayya ta duba wayarta ta ce "Ke ni fa tare nake da baƙo, bari na yi masa magana ya shigo". Babu tsammani Sumayya ta shigo tare da wani mutum, da ko ba a gaya wa Nabila ba, kamaninsa ya bayyanar mata da waye. Babu in da Viper ya bar kamanin mahaifinsa, shi ma haka yake dogo mai jiki, akwai alamar hutu a tare da shi, daga yanayin suturar jikinsa. Babu shiri Nabila ta miƙe, ta ce "Abbu sannu da zuwa, Sumayya ai da ni ki ka yi wa magana sai mu je mu same shi. Ta gyara masa kujera, ta ce "Bisimillah" sai dai ya daskare a wuri guda ya na kallon Nabila. "Jauhar ya na ganki a nan kuma?" Sumayya ta ce "Ba jauhar ba ce ai, wannan Nabila ce" "Ya za ki ce mini ba jauhar ba ce ba?" Nabila ta ɗan yi murmushi, ta ce "Abbu ni sunana Barrister Nabila Yusuf maitama, ita kuma sunanta Fatima Bashir Azare. Ka zauna dan Allah" ya zauna a hankali ya na bin Nabila da kallo. Ta kawo masa ruwa, ta nemi wuri ta zauna ta ce "Abbu ya gida ya iyali?" "Alhamdilillah, amma idan ba jauhar ba ce ba, ya aka yi ki ke kirana da sunan da iyalina suke kirana da shi?" "Saboda na san tarihin rayuwar Viper, an sanar da ni komai" Ya jinjina kai ya ce "Kin yi abin da ya tabattar mini da be ke ce Jauhar ba" Nabila ta ce "Me na yi?" Ya ce "Jauhar ba za ta taɓa kiransa da sunan da ki ka kira shi ba na Viper" Nabila ta ce "Afuwan Allah ya sa ba laifi na yi ba?" Abbu ya ce "Ko kaɗan, ba ki yi laifi ba, amma ina cike da mamakin yadda ya zamana ba ke ce jauhar ba, duk da a zahiri ban ga bambancin naku ba" Nan Nabila ta labarta masa kaɗan daga abin da yakamata ya sani, game da alaƙarta da jauhar. Ta numfasa ta ce "Abbu, duk da mu yaranku ne, kun fi mu tunani da hangen nesa, amma iyayenmu maza kuna tafka kuskure. Da mahaifiyar Viper ta na raye, ko a gabanta ya kashe jauhar, da ya dawo ba za ta kore shi ba. Har mahaifin jauhar ya ce bai yarda zai kashe masa 'ya ba, amma Abbu kai ka kasa karɓar Viper. A lokacin da ƙaddara ta kai ni cikin rayuwar Viper, ya fid da ran samun sassauci a rayuwa. Ga ƙwaƙwalwars ta taɓu ga shaye-shaye fiye da da da ya din ga yi. Allah ne kawai ya bani sa'a a kansa, daga shi sai abokansa da su ka riƙe shi, su ka karɓe shi su ka sadaukar da ta su rayuwar, saboda su rayu da shi. Na yi iya ƙoƙarina a kansa ya dawo in da kake, amma yaƙi sosai yake fushi a kan abubuwan da su ka faru" Abbu ya yi shiru, cike da jimami da kaico a kan wasu abubuwa da ya aikatawa rayuwar ɗan sa. Ya numfasa ya ce "Haka ne, haƙiƙa ni mai laifi ne a rayuwar Al'amin, duk da ni na haife shi, na cancanci na nemi gafararsa, dan sai daga bayan nan na fuskanci a lokacin da ya lalace, watsi da na yi da shi, ba shi ne masalaha ba. Amma dan Allah babu yadda za ayi ku taimaka ku haɗa ni da shi. Zan yi duk mai yiwuwa na ga na gyara kuskuren da na aikata a baya. Sannan duk wani support da ake buƙata in sha Allah zan bayar". Nabila ta numfasa ta ce "Ina haɗaku zai sauke mini kwandon masifa, duk wani ƙoƙari da nake yi a kan shari'ar ku, zai iya mayar mana da hannun agogo baya. Ranar da na haɗaku a waya ma, sai da muka yi faɗa da shi sosai. Sannan duk da ka na mahaifinsa, idan na haɗaku na saɓa yarjejeniyar privacy ɗin sa, da aka ja mini kunne a kai. Abu ɗaya zan iya ce maka, shi ne ka din ga halartar kotu wurin gudanar da shari'ar sa, kuma a sakamu a addu'a, sannan in sha Allah zan cigaba da ƙoƙarin shawo maka kansa" Abbu ya yi shiru sannan ya ce "Na yi kuskuren biye wa zigar mace, da hawa dokin zuciya na wofantar da ɗa na, na riƙe na wani, ƙarshe na zama mara kima a idanunsu. Ki ba wa Al'amin haƙuri, ki gaya masa abbu ya na kewarsa". "In sha Allah zan sanar masa, kuma komai zai dai-dai ta, na yi maka alƙawarin bibiyarsa da ci gaba da tausar sa, kamar yadda ya jagoranci haɗa ni da mahaifina" Ya jinjina kai ya ce "Na gode muku sosai da sosai, Ubangiji Allah ya biya ku da gidan aljanna, 'yar jarida ke ma na gode sosai" Sumayya ta yi murmushi ta ce "Na gode sosai Abbu" Nabila ta tashi ta ce "Abbu ba ka sha ruwan ba, na saka order ma a kawo maka abinci" Yayi murmushi ya ce "A'a Alhamdilillah, bari na sha ruwan dai, kasuwa zan tafi" Nabila ta ce "Allah ya tsare hanya, in sha Allah za mu zo har gida mu gaishe ka" Ya ce "Da kuwa na yi farinciki da haka. Ai daga ke har Sumayyan, na zata zan ga manya, na ganku duk 'yan yara matasa, Ubangiji Allah ya dafa muku yayi muku jagora baki ɗaya, Allah ya raya mana ku, ya tsare ku daga Sharrin mai sharri" Su ka raka shi har gaban motarsa, sai sanya musu albarka yake yi, ya buɗe motar, ya ɗaukko kuɗi ya ce "Ga wannan kwa sha ruwa, na gode sosai" Nabila ta ce "Haba Abbu, ai Addu'ar da ka yi mana ma ta isa, mun gode sosai da mu da Viper a cigaba da sanya mu a addu'a" "Addu'a kullum cikin yin ta ake yi, amma sai kun karɓa, sai dai idan kyautar Abbun ce ba kwa so" da kyar su ka karɓa, ya yi ta yi musu godiya ya tafi. Bayan sun koma ofishin Nabila, Sumayya ta ce "Ohh su Abla sai ɓare-ɓare ake yi, an ga siriki" Nabila kawai ta girgiza kai, ta din ga jinjina maƙudan kuɗin da ya basu kyauta, mutumin da zai iya bayar da wannan kyautar kuɗin, lallai mutum ne mai rufin asiri. *** Laraba ta bawa ranar samu in ji hausawa, ta kasance ranar da za a ci gaba da sauraren shari'ar Viper. Kotu ta cika iya cika, da masu ƙara waɗanda ake ƙara, lauyoyi 'yan jaridu ƙungiyoyi kotun cike fal. Bayan an kira ƙarar su Nabila, aka fito da lakwari da aka aike da shi magarƙama a wancan zaman da kotu ta yi. Babban abin da ya bawa Nabila mamaki, bai wuce ganin barrister Naja'atu Bunkure a cikin kotun ba, duk da ta ji gabanta ya faɗi, amma ta dake ta adana mamakinta a zuciyarta. Ta fito ta gabatar da kanta, aka fito da lakwari, Nabila ta nemi Walid ya fito. Walid ya fito ya tsaya, ta dubi Walid ta ce "Ko zaka iya bayyana wa kotu sunanka?" "Sunana Muhsin Hassan, wanda ake kira da Walid". Ta nuna masa lakwari, ta ce "Ka san wannan?" Ya jinjina kai ya ce "Eh na san shi" "Ka san laifin da ake tuhumarsa da shi?" "Eh na sani, laifin ki san kai ne na matar Al'amin da ɗan cikinta" "Ka tabattar?" "Eh na tabattar" "Za ka iya shaidawa kotu abin da ya faru?" Walid ya gyara tsayuwarsa ya ce "Ranar da za a kasheta, ni na aro babur ɗin adaidaita sahu, kamar yadda Al'amin ya buƙata, da ni da shi da abokinmu liti, mu ka je asibiti. Likita ya dubata ya ce ta wuce lokacin haihuwar ta, dan haka za ayi inducing ɗin ta, amma idan bai yi ba tiyata za ayi mata. Ta ce tana son cin ƙosai, muka yi ta yawo bamu samu ba, na yi alƙawarin zan nemo ƙosai da sassafe na kai mata, daga nan mu ka ajiye su a gida, mu kuma muka wuce. Da sassafen da na je, na tarar da layin a cike da jami'an tsaro, wai an yi kisan kai" "Ka ga gawar jauhar da ciki?" "Eh, a kan idonmu aka fito da ita an rufeta a cikin ledar gawa, ta na zubar da jini". "Waye ya kira jami'an tsaro ya sanar da su abin da ya faru?" Walid ya ce "Ban sani ba gaskiya" Nabila ta yi godiya, Bunkure ta taso ta gabatar da kanta a matsayin lauyar lakwari, sannan ta yi suka ga shaidar Walid, cewa shaida ce mai rauni, tun da bai tabattar da ganin lokacin da lakwari ya kashe jauhar ba. "Ya mai girma mai shari'a, ina son kotu ta bani dama, zan yi wa Al'amin wasu tambayoyi" Viper ya fito ya tsaya, ya na tuna abin da ta yi masa a wancan lokacin. "Malam Al'amin, a haka ba ka yi kama da malamai ba, balle ace wa'azi ka yi wa su lakwari ba su ka ji haushi, suka kashe maka mata ba. Me zai haɗa mutum kamar ka da mutane irin su lakwari har su shiga gidanka, su kashe maka mata? Ko ka na ta'amalli da miyagun ƙwayoyi ne kai ma?" Tayi maganar tana tsare shi da idanunta. Ayshercool 08081012143 93 Har Nabila ta zaburo za ta yi magana, Baba ya ce "Amma kamar ƙoƙarin tabattar da mutuwar jauhar ake yi, wannan tambayar abin da ya shafe mu ne personal issue ne" Nabila ta yi carf ta cafe, da sukar abin da Bunkure ta aikata. Da haka dai aka saurari wasu daga cikin shaidun na ranar, aka sake ɗaga shari'ar. Viper ya din ga jin jikinsa wani iri, sai da ya fito ya tsaya su na gaisawa da Baban su jauhar. Bayan Nabila ta fito daga cikin kotun, ta samu wuri tana amsa waya, babu tsammanni Nabila ta ji an janyota baya, an riƙe damtsenta. Ta waiwaya ta ga Naja'atu Bunkure, ta yi wa Nabila wani munafukin murmushi ta ce "Sannu da ƙoƙari barrister Nabila, lallai na yadda da kirarin da ƙawarki take yi miki, na a lady of her words, the voice of voiceless. Kin yi alwashin kai ni ƙasa, ki na ta faɗi tashin ganin kin ga bayana. To kafin ki ga nawa bayan ni zan ga naki, sai na tabattar miki da wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi. Zan kunna miki wutar da sai ta ƙonaki har lahira, abu mai daɗi da ya sauƙaƙa mini komai shi ne, samun labarin ke yar uwar matar Viper ce, ki na kare mijin yar uwakki, da kuma neman hakkin jininta da ya riga ya tafi a banza a wofi, zan illataki da wutar zahiri da ta baɗini ta zuci, sai na tona asirin miyagun ayyukan Viper sun koma kansa, na kassara Rayuwarki yadda zai zame muku baƙin ciki goma da ashirin, kamar yadda ku ka tarwatsa nutsuwarmu da ni da uban gidana Indabo" Nabila ta saka hannu, ta buge hannun Bunkure daga damtsenta, sannan ta hankaɗata iya ƙarfinta ta nunata da yatsanta ta ce "Jinin 'yar uwata ya fi ƙarfin ya tafi a banza, ƙarya ki ke yi, kuma wutar da ki ke shirin kunnawa, reshe ne zai juye da mujiya, dan kuwa ke zai koma ya ƙona, daga ni har Al'amin ƙarafa ne a cikin wuta da babu abin da wutar da ki ka kunna ta isa ta yi mana. Jinin yar uwata bai tafi a banza ba, duk wanda ya saka hannu wurin zubar da jininta, sai jinin jauhar ya zame masa mummunar gubar da sai ta kai shi lahira". Nabila ta daki ƙirjinta ta ce "Gani gaki  Naja, ki tsammaci abin da zatonki da hangenki bai taɓa tsammani ba" tayi maganar ta na nuna Naja'atu. Sumayya ce ta hango abin da yake faruwa, Viper ya na can ya na magana da Baba cikin girmamawa, ya na tsugunne Baba ya riƙe hannunsa, ya na ta yi masa nasiha da bashi ƙwarin gwiwa, Alhaji mu'azzam har mamaki abin ya bashi, dama haka Viper ya iya ladabi. Karaf idanun Viper su ka sauka a kan na Abbu, da bai san ma Abbun ya zo kotun ba, gabansa ya yi mummunar faɗuwa, Baba ne ya kalli in da Viper yake kallo, shi kansa bai lura da mahaifin Vipern ba sai yanzu. Cikin hanzari ya nufe shi, shi ma ya nufo shi cikin sauri, Viper kuwa kawar da kansa ya yi daga kallon Abbu, zuciyarsa na ci gaba da harbawa da sauri. Suka gaisa Abbu ya ce "Malam Bashir kwana da yawa, kawai sai samun labari mu ka yi kun tashi, babu ko sallama" Baba ya ce "Wallahi kuwa, ai na yi laifi ayi mini afuwa, ashe ka zo zaman shari'ar Al'amin, kuma kawai sai ka ga Nabila ita ce lauyarsa" Abbu ya ce "Abin ya bani mamaki sosai ya ɗaure mini kai, duk wannan abun ashe Jauhar ta na da 'yar uwa, ban taɓa sani ba, ta hanyar yar jaridar nan ƙawarta sumayya muke magana, ta kaini wurinta, wallahi na razana sosai, Allah na zata marigayiyya ce" Baba yayi murmushi ya ce "Allah kenan, mai jujjuya lamarinsa yadda ya so" Viper ya bar wurin da zai ci gaba da ganin Abbu, saboda yadda zuciyarsa ke neman tsinkewa, sai azalzalarsa zuciyarsa take yi ya ƙarasa wurin da Abbu yake. Can ya hango Sumayya ta danƙo hannun Nabila, sai surutai take yi, fuskarta ta koma ja, da alama ranta ne ya ɓaci. Nufar su yayi da sauri, ya na tambayar su ko lafiya. Sumayya ta ce "Faɗa su ka yi da Naja'atu Bunkure" Cikin mamaki ya ce "Faɗa kuma?" "Eh" Ya ce "Meya haɗa su?" "Wallahi ban sani ba, ƙarar da aka yi bayan taku na tsaya saurara, na yi picking wani abu a cikin rahotannin da zan yi yau, kawai da na fito na gansu su na cacar baki" A nutse ya kalli Nabila da take ta huci ya ce "Meya haɗa ki da ita?" Shiru Nabila ta yi ta kasa magana. "Ina tambayar ki menene?" Still ta kuma yin shiru, sai sauke ajiyar zuciya take yi. Ya ce "To wuce mu tafi" Ya sakota a gaba su ka fito harabar kotun, a wannan karon har da Alhaji mu'zzam kankarofi suke tare da su Abba, Abban ya gabatar wa da Alhaji mu'zzam Abbu mahaifin Viper. Gaba ɗaya hankalinsu ya dawo kan su Viper, da su ka taho fuskar Nabila sam babu annuri. Rige-rigen tambaya su ka fara yi, ko lafiya Nabila take cika ta na batsewa. "Ya aka yi ne, meyafaru?" Baba ya tambayeta cikin kulawa. Kawai ta durƙusa ta fashe da kuka. Viper ya ce "Wai ke wace irin yarinya ce, wannan ai halin yarinta ne, barrister ce fa ke, a harabar kotu ki zauna ki na kuka saboda wauta da abin kunya?" Alhaji mu'azzam ma ya ce "Nabila menene, kar ki ɗaga mana hankali mana" Abbu ma cewa ya yi "Idan yanayin yadda shari'ar ya gudana ne bai yi miki ba, ki yi haƙuri mu je a ci gaba da addu'a da neman ɗaukin Ubangiji" Abbu na fara magana, Viper ya yi ɗif, ya juya ya bar wurin. Abin da Viper ya yi ya ƙara wa Nabila takaici, cikin mamaki Baba ya ce "Ya haka kuma?" Abbu ya girgiza kai ya ce "Rabu da shi kawai, komai yayi mini na cancanci hakan" Still wani mamakin ya sake cika Alhaji mu'azzam, ya na mamakin wane irin mutum ne Viper haka, baban na sa ma. A dai-dai lokacin liti da Walid su ka ƙara so gaban Abbu, su na zuwa suma durƙusawa su yi a gaban Abbun, cikin matuƙar girmamawa su na gaishe shi tare da Baba. Abbu ya dafa kafaɗunsu ya na amsawa. "Ya ƙoƙari ya fama da Al'amin" Walid ya yi murmushi ya ce "Babu fama Abbu" "Ina ta godiya Ubangiji Allah ya saka muku da mafificin alkhairi, dan Allah a ci gaba da bashi haƙuri, ace ya yafe wa Abbansa" Liti ya ce "In sha Allah" Walid ya kalli Nabila da take kuka ya ce wa Sumayya "Me ya sameta?" "Shagwaɓa mana" Sumayya ta bashi amsa ta na kallon Nabila. "Mai zamani ne ya yi mata wani abun kenan?" "A'a faɗa su ka yi da Naja'atu Bunkure, ban san me ta yi mata ba dai" Liti ya ce "Ai matar nan shegiya ce, wani abun ta ƙudurce a ranta za ta aikata, mussaman yanayin tambayoyin da take yi a kotun nan" Abbu ya ce "Ki kwantar da hankalinki, kar ki damu kin ji jauhar, in sha Allah za ayi nasara" Baba ya ce "Nabila dai". Abbu  ya ce "Ni jauhar nake gani, duk ɗaya ne a wurina" Alhaji mu'azzam ya yi murmushi ya ce "Nabila akwai ƙoƙari da jajircewa, sai faɗa da tsiwa, unlike jauhar, so calm ba ta da hayaniya" Abbu ya ce "Dan Allah dai ko da tsayayye wannan ma mu na riƙo, a taimake mu a bamu, ta maye mana gurbin jauhar da muka rasa". Dumm gaban Alhaji mu'azzam ya buga, Baba kuwa ya ce wa Abbu "Ai a yanzu dai wannan ba ni da iko da ita, akwai ƙura a kanta". Nabila ta ce "Baba ni na tafi" "To kya tafi ki na kuka Nabila, ko in tafi da ke can gida?" Ta girgiza kai alamar a'a ba zata bi shi ba. Ya ce "Hafsa kullum cikin zancenki take Nabila, yanzu ina zaki tafi?" "Gida wurin Abbana" Ya ce "Dama ai Abbanki ne, ban ce nawa ba ne ba" Alhaji mu'azzam ya ce "Ko mu tafi na ajiyeku a hanya?" Liti ya ce "A'a ga mota can da security ɗin da suke kula da ita ai, zamu rakata" Alhaji mu'azzam ya yi murmushi, ƙiri-ƙiri Viper suke taya wa kishi, sun manta da saka hannunsa aka ba wa Nabilan security. Baba ya ce "To Allah ya kiyaye hanya, ina nan tafe wurin Abban naki, ki gaida mutanen gidanku" Sumayya ta ja hannunta su ka yi gaba, Abbu ya kalli Baba ya ce "Ni ranar da na fara zuwa office ɗin ta, na zata Jauhar ce, ta yi mini wani bayani da ban gama fahimta ba, yaya aka yi Jauhar take da yar uwa bamu taɓa sani ba?" A lokacin Abba ya warware masa komai, har yadda aka yi auren Jauhar da Al'amin, da yadda ya mayar wa da Alhaji mu'zzam kuɗin aurensa, da tsamar da suke yi yanzu da Major a kan Nabila, ya na son ya karɓi 'yar sa, ko yaya ya zauna da ita kafin ta yi aure, amma ya san major ba zai taɓa bari ba, ita kanta ba zata yadda ba dan ya ga tsanar iyalinsa muraran a idon Nabila. Abbu ya ce "Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya yi gaskiya da ya ce bai bar wata fitina a bayansa mafi cutar da maza ba, dai daga mataye. Sai yanzu na ƙara yadda da mata su ne ƙashin samar da duk irin al'ummar da suke so, na gari ko kuma akasin haka. Wallahi Alhaji Bashir, ina cikin matsananciyar nadamar wofantar da rayuwar Al'amin, a ganina haka ne mafita, matar nan ta din ga zigani ina hawa kai, 'ya'yana na cikina su ka rayu kamar bayi, duk rufin asiri da nake da shi amma rayuwar Al'amin ta ƙare a haka. Ina baƙin ciki haɗuwata da shi ta ƙarshe da ya dawo daga prison, ya na tambayata ya aka yi da matarsa, ban saurare shi ba balle na yi masa uzurin ba zai iya kashe jauhar ba. Na ji kunya da kai a matsayin ka na mahaifinta ba ka aminta zai kasheta ba. Na tafka kura-kurai duk a dalilin rashin dace da mace ta gari". Sai su ka ɓuge da hira, da jajantawa juna, sosai su ka yi wa Alhaji mu'azzam a kan gudunmuwar da ya ba wa rayuwar Nabila da Viper. Har gidan Abba su ka kai Nabila, sannan su ka watse, sumayya ma ta tafi wurin aikinta. Azahar ce lokacin, kuma dama ba salla za ta yi ba, ta na period, ta tafi falon Abba. Ya na tare da Mama, Nabila ta yi sallama, Abba ya amsa, mama ta haɗe rai. Ta dire jakarta, ta ware veil ɗin kanta, ta haye kan doguwar kujera ta kwanta. Mama ta yinƙura za ta yi magana, amma Major ya kalleta, hakan ya tilasta mata haɗiye maganar da ta yi niyyar yi. Nabila ta ci gaba da kuka, amma Abba bai kulata ba, ta ce "Abba wai ba zaka kula ni ba?" Ya yi mata shiru. Tashi mama tayi ta bar masa ɗakin, ganin magana take yi da shi mai muhimmanci Nabila ta zo ta kwanta tana kukan rashin mutunci. Doguwar ajiyar zuciya da ta sauke, ya sanya ya kalleta, bacci ta yi, hakan ya tabattar masa akwai gajiya a tare da Nabilan. Ya gyara mata hannunta, ya na kallon fuskarta, wadda take sak ta chubaɗo. Kawai ya din ga hango ina ma duka ya ɗauke su ya riƙe, da Nabila da Jauhar, ɗaya lauya ɗaya likita, da sai ya fi alfahari da hakan, amma haryanzu bai ga alfanun tsaya wa Viper da Nabila ta yi ba, duk da kasancewarsa ɗan daba, kuma da ya ɗan bibiyi abin da ya faru, babu wani history mai kyau a kan Viper, ban da dillancin ƙwaya da sara suka, sai kuma tserewa daga prsion bayan an kama shi da laifin kisan kai, kuma wai daga baya an hana kama shi. **** Mahaifiyar Abdul ta kasa nutsuwa gabaki ɗaya, ta na ta ƙoƙarin yadda za a bayar da belin Abdul a sake shi, amma abu ya ci tura, duk da irin tayin kuɗaɗen da ta sanya aka din ga yi wa masu ruwa da tsaki a kan shari'ar ɗan nata, amma kuɗi su ka ƙi tasiri, alamu su ka nuna da gaske so ake a hukunta Abdul. Ba ita ba, hatta abokan Indabo, sun yi iya yin su amma aka nuna musu ba za yiwu ba. Sau ɗaya ta je ta ga Abdul, hankalinta ya yi mummunan tashi, gashi dai a wuri na musamman yake, ba wai haɗa shi aka yi da sauran fursunoni ba, amma gaba ɗaya ya fita daga hayyacinsa. Ya ƙara ramewa, gashi mutum ne mai kufan gashi, saboda haka tuni gashi ya cika masa fuska. Duk da ana kula da shan maganinsa ya na samun abinci, amma ba irin wanda yake so ba. *** Da la'asar Nabila ta tashi, ta yi wanka, ta ɗauki abin da za ta ɗauka za ta fita. Baba Magajiya ta tare ta ta ce "Arfa, duk yadda major yake kaffa-kaffa da ku, mussaman ke yake saka miki ido da kula da ke, amma ya zuba miki ido, ki na shige da ficenki, mutanen gidan nan har da maƙwabta su na ta surutu a kan hakan, yakamata fa ki kula ki yi wa kanki faɗa". "Baba magajiya, Abba ya san ko nan da bangon duniya zan fita, Abba ya na da yaƙinin ba zan lalace ba, ba zan yi abin da zan cutar da kaina, ko na janyo masa abin kunya ba. Kar ki manta har ƙasar ƙetare na fita na yi karatu ban lalace ba, in sha Allah ba zan baku kunya ba" "Abin kunya na nawa kuma, banda wanda ki ke aikatawa yanzu? Kwana a in da ki ka ga dama, yawo da ƙaratan 'yan daba me ya rage kuma?" Nabila ta kalli mama cikin nutsuwa ta ce "Hajiya mama yaushe ki ka fara damuwa da ba na kwana a gida ne? Tun yaushe ki ke yi mini fatan abin kunya? Ni ban aikata abin kunya ba, ba kuma na fatan na aikata, Nasir shi ne mai abin kunya a ƙugunsa, da ya canza mota ya gama gini, yake wadaƙa da kuɗi wanda ya wuce samunsa ba ki tuhume shi ba, Abba ya yi yinƙurin tuhumarsa ki ka hana ki ka kare shi. Ki daina shiga harkata tun kafin na nuna wa duniya waye ɗan naki" Baba magajiya na takaicin yadda mama ta daɗe da zubar da mutuncinta da tun Nabila na jin nauyinta ta na girmamata, har an kai ƙadamin da ta daina ɗaga mata ƙafa. Bayan ta fita wayar Viper ta kira, liti ya ɗaga. Ta ce "Ina mai wayar?" "Bacci yake" ya amsa mata kai tsaye. Ta ce "Bacci da yammacin nan, shikenan" Rabon Nabila da gidan har ta manta, liti ta tarar da ɗan mama a tsakar gidan su na hira, amma rabin hirar ɗan mama zagi kawai yake sha a wurin liti. Amsa sallamar su ka yi, Nabila ta ce "Ɗan mama ka yi free kenan?" "Eh belina aka bayar ai, dama za mu tattauna da ke, nima zan iya bayar da shaida" Nabila ta yi murmushi ta ce "Shikenan, ina Oga?" Ya na cikin ɗaki, ya na ta aikin danna waya. Nabila ta yi murmushi ta shiga ta tarar da shi, ya tashi daga baccin, ya na zaune ya na ta danna tab. Gefensa duk abin sauran sigari da ya sha. Ta zuba masa ido, ya cigaba da abin da yake yi, sai da ya kammala sannan ya kalle ta ya ce "Daga ina ki ke?" Ta kwaɓe baki ta ce "Gida" "Wai meyasa ba kya ji ne? Ke duk wani abu da za ki aikata, ace ba ki kyauta ba, kin san shi kuma za ki aikata. Kin sani sarai you are not safe, an kai ki in da zaki zauna, an baki wanda za su din ga fita da ke, saboda tsaronki, amma sai yawonki ki ke yi yadda ki ka ga dama, tarar aradu da ka fa ki ke yi?" Tayi shiru kamar gaske ta na saurarsa. "Meya haɗa ki da Naja'atu Bunkure, har ku ka yi faɗa ɗazu a court, kar ki je da gayya take yi miki abin da za ki yi reacting, ta samu kafar cutar da ke" Nabila ta ja numfashi ta ce "Ni matar nan za ta kalli tsabar idona, ta ce mini wai jinin 'yar uwata ya tafi a banza? Ban san ya aka yi ta samu labarin cewa jauhar sisterna ce ba. Da fari na fara karaya, jin yadda take zaƙulo tambayoyi a kotu, duk da na yi tsammanin hakan, amma abin da ta gaya mini, tamkar ta yi mini allura ne,  jinin jauhar sai ya zame musu bala'i ya zame musu guba mai mummunan hatsari" Ya ajiye tab ɗin ya ce "Haka ta ce Jinin matata ya zuba a banza?" Ta jinjina masa kai. Ya numfasa ya ce "Haryanzu su na wasa da ni, daga ita har ubangidanta, daga nesa suke hangena a cikin wutar, zatonsu hannayensu za su iya jure zafin da na ɗauka su ɗaukko ni, na san abin yi" Nabila ta gyaɗa kai ta ce "Ko ni sai na ba wa matar nan mamaki, shashasha kawai" Yayi shiru yana juya maganar, da jin zafin abin da Nabila ta ce Bunkure ta faɗa, kamar ita aka gaya wa. Kamar wadda aka mintsina ta ce "Yauwwa kai kuma" ya juyo ya kalleta tamkar uwar da take shirin yi wa ɗanta faɗa. "Viper ka bani haushi, zan iya cewa abin da ka yi ya kusa fin abin da Bunkure ta yi mini" tsuke fuska ya yi ya na kallonta. "Ai ko za ka cinye ni ɗanya sai na faɗi abin da ya kawo ni. Abbu da kansa ya je Office ya same ni, ba aike ba a kanka, ni na ce ma ya zo kotu ya din ga ganin yadda shari'ar take gudana, ya damu ya damu saboda kai, amma a gaban mutane, a gaban kowa da kowa ka yi tafiyarka ka bar shi, me ka aikata kenan? Nuna wa duniya cewar mahaifinka bai isa da kai ba ko kuwa? Kai ka ce har da bijire masan da ka yi Allah yake jarabtarka, so ka ke wani bala'in ya same mu ne a sanadin wulaƙanta iyaye?. A cikin Alƙur'ani mai tsarki sau nawa Allah ya maimaita yi wa iyaye biyayya? Ka daina kallon ya yi maka laifi, kai sai Allah ya hukuntaka da ƙaurace masa da ka ke yi. Nan fa ni ka zaunar da ni ka na yi mini nasiha, kai meyasa ba za ka yi aiki da nasihar ba" "Ke shut up! Kullukum ra'in, wa kullukum mas'ulun an ra'iyatihi, sau nawa Abbu yayi wannan tunanin a game da ni? Ya wofantar da mu ni da ɗan uwana, an kashe shi ya ce ni ne sila, a duniya ina cikin 'ya'ya masu tsananin ƙawazucin iyayensu. Kin san sau nawa daga gidana kan sallar asuba nake tafiya unguwarmu, dan ayi sallar asuba a idar ya wuce na ganshi na ji ƙamshin turaren sa, saboda ƙamshin ya na tuna mini lokutan da su ka gabata mu ka rayu cikin farin ciki da son juna. Babu nasiha tsakanina da shi, babu rarrashi sai zagi hantara da kuma kora, alhalin ina kallon ya na ta haƙilon alkinta rayuwar yaran matarsa? Ni kuma ina yawo babu sana'ar kirki da zan kula ma da matar da ya aura mini, ki na tunanin ko na fi kowane ɗa lalacewa a duniya, idan mahaifiyata na da rai watsar da ni za ta yi?. Kin san sau adadin zuwan da nake yi in da yake ya na korata, kamar wani kare, kin san cin mutuncin da ya yi mini a lokacin da na baro prsion na je in da yake, ya kore ni ya ci mutuncina wai ba ya ƙaunar ganina na kashe jauhar, me ya rage nake nema a wurin Abbu ne tun da ya furta ba ya ƙaunar ganina? Har cikin zuciyata ina son mahaifina amma ba zan ɓoye miki ba, gaba ɗaya ya sire mini, uwata da ta mutu ma Allah ya raya ni, ɗan uwana mai tausayina da aka kashe shi, shi ma Allah ya raya ni. Dan haka zan iya rayuwata ko babu Abbu. Da ya tallafi rayuwata da wataƙila duk wannan azabar ban sha ta ba a rayuwa. Ki gaya masa ya rayu da waɗanda yake so, halarta wurin shari'ata ma na yafe ya zauna ya huta, Allah zai wanke ni" Nabila ta yi masa ƙuri da ido, har ya yi gama, idanunsa su ka yi jawur kamar an zuba masa gauta, dama ga sigari ya sha. Ta ja ajiyar zuciya ta ce "Ni da kai ta wata fuskar tamkar jirgi ɗaya ne ya kwaso mu, amma sai dai akwai in da ƙaddarorinmu su ka sha bamban. Vi" ta kira shi a sanyaye. Ya kawar da kansa gefe, ya na ta sauke ajiyar zuciya. "Ka kalle ni mana magana za mu yi"ya ƙi waiwayo wa. Ta zagaya saitin in da ya kawar da kansa, hawaye ya cika masa ido. "Vi dan Allah kar ka yi kuka, ka yi haƙuri, amma kasancewar ka abu mafi soyuwa a wurin 'yar uwata ina fatan har a lahira ka kasance da rahamar Allah, ban yi maka wannan maganar dan na ɓata maka rai ba, lokuta da dama sai Allah ya jarrabi bawansa kafin ya yi masa wani tagomashi na alkhairi. Dan Allah ka yi haƙuri, amma ba zan haƙura da rarrashin ka ba, a kan ka daidaita da Abbu. Iyayenmu duk da sun dace da mataye na gari, da ba su aikata wani abun ba" Ya haɗiye wani abu mai ɗaci ya ce "Tashi mu je na mayar da ke barrack, na san kan ki koma duhu yayi, kuma idan na sake ganin kin zo nan sai na ɓallaki na gaya miki" "Ba zan sake zuwa ba, but smile mana dan Allah, kar mu tafi ka na huci, na ga ka ɗauki zafi da yawa" Viper ya sake tsuke fuska ya ce "Tashi mu tafi" kamar yarinyar goye, ta maƙale kafaɗa ta marairaice ta ce "Dan ka yi murmushi Vi, ba na son wannan mood ɗin naka" tashi ya yi tsaye, ya ɗaukko face mask ɗin sa ya saka su ka fita. Su na tafe a hanya, ta na ta yi masa hira, tun ya na basarwa har kuma ya saki jikinsa, har da yin murmushin. Nabila ta sha faɗa wurin madam Halima, saboda rashin jin ta da taurin kai, na yadda take wasa da rayuwarta. Madam Halima babu hausa sosai, gashi wai a dole sai ta yi wa Nabila faɗa, sai da Viper ya yi murmushi, dan Nabila ba ta san faɗa, ta haɗe rai. *** Abdul ya cika sati uku a gidan kaso, amma duk ya firgice kamar ya kwashi shekaru a tsare, duk da halin da yake ciki, bai hana shi ganin ramar da matarsa ta yi ba, ga cikinta ya fara tasawa babban fatansa shi ne Allah ya sa tun da an ce za ayi masa sassauci ramma kar ta haihu ya na tsare. Ba tare da sake yin wani dogon jawabi ba, kasancewar ya riga ya amsa laifinsa, lauyoyin sa su ka nemi a ƙara sassauta masa, tun da ya amsa laifinsa ba tare da ya wahalar da shari'a ba. Alƙali ya yanke hukuncin a yi wa Abdul bulala ashirin, a kai shi gidan yari tsawon watanni biyar, da aiki mai wahala, sai kuma tara ta zunzurutun kuɗi naira miliyan biyar. Kasancewar a chamber alƙali ake shari'ar, ba a cikin kotu ba, mahaifiyar Abdul ta marairaice a kan ya ƙara sassauta masa. Alƙalin ya dubeta ya ce "Madam, mutanen nan fa sun yi muku adalci, da ba kotun shari'a su ka kawo ƙarar nan ba, ke kin san laifukansa sun fi ƙarfin hukuncin da aka yi masa, dan haka babu wani sassauci ko ɗaga ƙafa da za a kuma yi masa. Ku je ku yi ta haifar yara babu tarbiyya ku na sakin su a cikin al'umma su na fasadi a bayan ƙasa, ba tare da kun damu ba, iya yarinyar da ya ketawa haddi ba 'ya ba ce? Tarar ma idan ba zaku biya ba, sai ya je yayi zaman shekara bakwai a gidan yari, hakan ya zama izina da kuma darasi ga saura" Ana gama zaman, Nabila ta janye ramma daga kotun, aikuwa su na tafe ta na kuka, mussaman jin za a dake shi, ga kuma aiki mai wahala an ce yayi a gidan yarin. A waya Nabila ta kira Viper ta ce masa ta tafi da ramma barrack, washegari ta mayar da ita wurin mama, saboda ta ɗan samu nutsuwa. Mama kuwa duk da ba haka ta so ba, amma ta samu sassauci daga baƙin ciki da kuma raɗaɗin da zuciyar ta take yi mata. Ganin gigicewa da tashin hankalin da majaifiyar Abdul ta shiga, maman ramma ta ce "Kamar haka, haka na shiga tashin hankali, lokacin da ya ketwa 'ya ta haddi, kuma na rasa mai taimakona, Alhamdilillah ko iya haka na samu raguwar wata azabar da nake ji". *** Rahama ta kasa bacci, ta kasa cin abinci, nan Nabila ta ƙara tabattar da soyayya bala'i ce wani lokacin. Duk wannan bala'in da ake yi a kanta, ita hankalinta ya na kan mijinta. Haka Nabila ta yi ta aikin rarrashinta. Washegari ta kashe wayoyinta, ta ɗauki ramma aka kai su prison. Sai dai aka sanar musu, Abdul ba zai iya fitowa ba, Albarkacin ID card na aiki, da yadda Nabila ta fara tashe, aka ba su damar shiga cikin prison har ɗakin da Abdul yake. "Subhanallah" ramma ta furta, ganinsa a kwance ruf da ciki, bayansa a farfashe saboda bulalar alƙali da ya sha. Ta ƙarasa in da yake da sauri, ya ɗago da kyar, jikinsa ya na karkarwa saboda zazzaɓi, Abdul zai iya cewa da wayonsa babu wanda ya taɓa dukansa, amma yanzu ga shi ya sha duka, hakan ya haifar masa da zazzafan zazzaɓi. "Abdul" ta faɗa a raunane ta na kuka. "Rahama zafi, bayana kamar ana ƙona ni" "Ka yi haƙuri Abdul, dan Allah ka yi haƙuri, ban ma san me zan ce ba" tayi maganar cikin kuka. "Ai an sassauta mini, ta wani fannin na ji daɗi da wuri zan fito in sha Allah, ni zan karɓi haihuwar ki da kaina" yayi maganar yana kwanciya a jikinta. Ta haɗiye yawu mai zafi, ta ce "Abdul da sun bi ta tawa, da na daɗe da furta musu na yafe maka, babu yadda mu ka iya, ƙaddaramu ce ta zo a haka. Amma ka yi haƙuri na yi maka alƙawarin duk rintsi idan ka fito in sha Allah mu na tare" Ya ɗago da kyar ya kalle ta ya ce "Are you sure, kar ki saka mini rai fa" "Na tabattar in sha Allah" "Wallahi ina sonki sosai rahama" Nabila ta na tsaye ta na kallon ikon Allah. **** Viper ya na ta shiri zai je wani aiki na musamman cikin sirri, wayarsa ta fara ringing, bai damu da duba waye ba kawai ya ɗaga. "Aminu Viper" "Ma'aruf Indabo" ya amsa masa kai tsaye. Indabo ya ce "Ban yi mamakin saurin ɗaukar muryata da ka yi ba, kai a nan ka dage ka haɗa kai da kankarofi a kan lallai sai kun ga bayana, yanzu ka kafe kai da fata, saboda yar matsiyata ƙanwar Nura guduma, an kai mini ɗa gidan yari, to bari murna karenka ya kama Zaki mai zamani. Za a sake ni daga ɗaurin talalar da aka yi mini, sannan ka shirya abubuwan da ka iya biyo baya da ba ka yi tsammani ba. Za a ci gaba da zaman kotu a kan shari'ar matarka, amma ka sani reshe ka iya juyewa da mujiya, ka tsammaci abin da ba ka taɓa zatonsa ba a kotu". "Gargaɗi ka ke yi mini? Ko alhinin kar asirinku ya tonu a kotu, idan gargaɗi ka ke yi mini kar na kama sunanka, ka kwantar hankalinka, ai an san da wuyan biri ake ɗaure shi a ƙugu, kai tsaye waɗanda su ka kashe matata kawai za a hukunta, sannan ka din ga sassauta lafazinka idan ka na magana da ni, saboda ni ke da makami mai linzamin ƙarasa tarwatsa rayuwar iyalinka, idan ka ƙi ji ba ka ƙi gani ba. Na san babu abin da za ayi maka ko da kuwa an ambaci da saka hannunka a ta'addancin da aka yi mini. Zan yi dragging ɗin ka zuwa kogon da ramina yake ne, na yi ta azabtar da kai da dafina, zuwa abin da hali zai yi. Amma ina P.A ɗinka yake ne? Kwana biyu ba a ganin gilmawarsa yakamata ka yi tunani a kan wannan" ƙit ya kashe wayar. Ayshercool 08081012143 94 Viper ya ɗan ja lokaci ya na kallon wayarsa, ya na tunanin mai indabo yake shiryawa, da har ya samu ƙwarin gwiwar kiransa ya na yi masa surutan iska. Kodayake bai kamata ya ce surutan iska ba, domin kuwa a rashin imani irin na indabo babu abin da ba zai iya aikatawa ba. Lambar Nabila ya yi ta kira, amma a kashe ba ta shiga, dan haka ya haƙura ya ci gaba da shirin fita. Ramma ta yinƙura ta ce "Bari mu tafi, na san ba dan albarkacin Anty Nabila ba, babu yadda za ayi a bari na shigo har na ganka, Allah ya baka lafiya ya baka ikon cin jarrabawar nan. Ba an hukuntaka da an tsaneka bane ba, ina fatan tuban da ka yi ya zama taubatan nasuha, kuma wahalar nan Allah ya sa ta zame mana kaffara baki ɗaya mijina" ya ɗago ya kalleta ya ce "Kai, rahama baki taɓa kirana da sunan da na ji yayi tasiri har cikin zuciyata kamar yau ba, da har nake jin eh lallai kin yafe mini ba. Yanzu kin yadda ni mijinki ne?" Ta yi ƙasa da muryarta ta ce "Ai zamantowarka mijina tuntuni na yarda da wannan, da ban yadda wannan cikin ya samu ba" murmushi ne ya suɓuce masa, ta tashi ita ma ta na murmushin, ta fita daga ɗakin har ta fice ya na daga ruf da ciki ya na kallonta, duk wannan wahalar da yake sha, ko sau ɗaya bai ji wani abu daga son da yake yi mata ya ragu daga zuciyar sa ba. *** Nabila ta biya ta ajiye ramma a gida, sai dai ramma ta fuskanci mama ta sassauta fushin da take yi da ita, saboda ta ɗan samu sassauci saboda hukunta Abdul da ta ga an yi. Barrack Nabila ta koma, dan ita kanta ta ɗan tsorata da musayar yawu da su ka yi da Najar bunkure, dan ta san ba imani ta cika ba, amma da ta tuna da furucinta na cewar Jinin jauhar ya tafi a banza, sai wani nannauyan abu ya soki ƙirjinta. Kusan da ciwon mara ta wuni, daurewa kawai take yi, su ka ci abincin dare tare da madam Halima, ta na ta ba wa Nabila labarin yadda aka kashe mijinta, da yadda ta zama soja. Nabila ta ce "Taɓ sannu da ƙoƙari Mummy" Madam ta ce "Daughter ke ma fa za ki iya zama sojan nan, ki zama military lawyer. Ga Mijinki soja na musamman ke ma haka" Ta kalleta ta ce "Waye mijin nawa?" "Ahh Viper mana" Nabila ta ce "Taɓ ba zan iya ba, gara na auri civilian irina, ni fa idan ki ka ɗauke tsiwa daga nesa nesa, ko gadin ƙofa ba zan iya balle wani soja, ko 'yar agaji ba iyawa zan yi ba. Da ne da bani da hankali na ce wa Abba soja zan zama, ya ce ban isa ba, daga baya na fuskanci da na zama sojan, ba za ayi abin arziki ba" Madam ta ce "Haba dai, kar ki bayar da ni mana, and kuma ba soyayya ku ke yi da Viper ba, ba shi ne zai aure ki ba?" "In ji wa? Mijin sister na ne fa" "Ehenn your sister is late, and ba haramun bane a addinin musulunci, soyayya fa ku ke yi ina kallonku" Nabila ta ɓata fuska ta ce "Mummy ba ki gani dai-dai ba, ni fa marata ce take ciwo, gashi zuciyata sai tashi take yi kamar zan yi amai" Madam ta ce "Sannu, ko za ki je ki kwanta?" Abu kamar wasa Nabila ta gagara bacci, sai da madam ta kaita clinic, aka yi mata allurai ta dawo ta kwanta. Cikin dare madam Halima ta tashi ta na sallar dare, ta din ga jin ringing ɗin wayar Nabila a falo, ta fito ta kashe, ta ga Vi snake. Ta ɗaga ta ce "Snake ka ke kiran yarinyata cikin dare haka me za ta yi maka?" Viper ya yi murmushi ya ce "Important issue ne shiyasa na kirata" "Salon ka hanata bacci, ba ta jin daɗi ne, bamu daɗe da dawowa daga clinic ba, ta samu bacci menstrual cramps ne yake damunta, ta na ta ciwon mara ta sha allurai dai, har da kuka dan sangarta. This your wife is not brave at all, lazy citizen" Murmushi Viper ya yi ya ce "Thank God ke ki ka faɗa ba ni ba, ayi mata sannu sai da safe". "To shikenan sai anjima" ta kashe mata wayar ta ajiye. Da safe ta ga Nabila ta shiryo cikin uniform ta ce "Kin ji sauƙi za ki iya zuwa aikin ne?" Nabila ta ce "Eh Mummy, da sauƙi sosai" Ta ce "To Alhamdilillah, come and have your breakfast". "I have no appetite, zan samu wani abu na ci, zan haɗu da Joseph a bakin gate, zan tafi". Suka yi sallama Nabila ta fita. Babu shari'ar da za ta halarta, dan haka ta na office ɗin ta, ta na ta aiki, zuwa ƙarfe sha ɗaya na safe, ta ji yunwa ta addabeta, ta ajiye aikin ta fita. Ta fita babu daɗewa sai ga Viper ya zo. Ya tarar ba ta nan, amma yadda ta bar ƙaramar wayarta da jakarta ya tabbatar masa da ba nisa tayi ba. Ya ƙarasa gaban teburin, ta ajiye cake ga kofin tea da madara da milo, da alama tea za ta sha, ya janyo drowern teburin, nan ma ya iske gugguru da tarkacen alawoyi. Ya girgiza kai, a dai-dai lokacin ta buɗe Office ɗin ta shigo, hannunta riƙe da leda. Ta ce "Binciken me ka ke yi mini waye ya baka iznin shigo mini office ma?" Tayi maganar tana ƙarasawa. Ya ɗago ya kalleta ta ga idanunsa jawurrr. "Ba ciwon mara aka ce ki na yi ba, amma ki ke cin wannan kayan zaƙin?" Yayi maganar ya na tsareta da idanunsa. "Waye ya ce ina ciwon mara?" Tayi maganar ta na zaro ido. "Madam, na kira jiya da daddare ta ce kun je asibiti, and yanzu kalli tarkacen abin da ki ke ci, ko tausayin kanki ba kya ji. Duk ranar da ki ka zo haihuwa zaki yi bayanin wannan zaƙin da ki ke ci ba yau ba gobe saboda basir" Murmushi ta yi ta ce "Ba sai in zan haihun ba, adopting ɗin baby kawai zan yi, banda haihuwa dan tsoro nake ji, akwai wahala, idan ma zan haihu irin ɗayan nan is ok" "Saboda ke haka aka yi miki? Ko kuma dan ke ki ka tsara wa kanki rayuwa?" Ta ce "No ai yarjejeniya za mu yi da babyna kafin mu yi aure, banda haihuwa" ƙura mata ido yayi, ya na lumshe su a hankali. Ta ce "Bari na wuce, kai ma sai na sammaka, ko ya aka yi ma ka san cin zaƙi na saka basir..... Kan ta ƙarasa maganar ya ce "Am once married" Ta ce "Eh haka ne, matsa na wuce to, bobon zan sammaka ko za ka ci gugguru. Wato bincike ma ka yi mini, duk ka kwaso mini kaya, ka ajiye a kan tebur" tahowa yayi zai faɗo a jikinta, ta ja baya kaɗan a tsorace. Ya dafe teburin ya na sauke numfashi. Jiki a sanyaye ta ce "Vi" ya ɗago jajayen idanunsa a wahalce ya kalleta. "Again? Me ka je ka sha ne? Na za ta ka daina gaba ɗaya, sai abin da ba a rasa ba. Ka yi shaye-shaye kuma ka taho hanya ba ka tsoro wani abu ya sameka? Me aka yi maka ma ka je ka sha kayan maye? Waye ya ɓata maka rai" Ya kuma jan numfashin, ya na lumshe ido. A hankali ya ce "Am so much thirsty, ina shan baƙar wahala, saboda daina ta'amalli da kayan maye. Idan ƙishirwar shan ta taso mini, sai na ji kamar zan bar duniya idan ban sha ba, is not that easy rabuwa da shaye-shaye" yayi maganar kamar zai faɗi ya na lumshe ido. "Me ka sha?" Ta tambaye shi cikin damuwa. Fito mata da dogon harshensa ya yi, duk ragowar farin ƙwayar da ya sha. Ta ce "Guda nawa ka sha?" Ya ɗago mata yatsunsa guda uku. Ya ce "Uku ne kawai, ban sake yi wa kaina allura ba ai, tun da ki ka shigo rayuwata, ki ka bani ƙwarin gwiwa da tabbacin zan iya sake rayuwa kamar kowa. Kin san da ba sa ɗaukata, yanzun ma ban yi tunanin za su ɗauke ni ba, sai da na zo nan gabanki, kawai su ka fara ɗibata, dole sai sun tona mini asiri" yayi maganar yana murmushi tare da layi. Ta numfasa ta ce "Muje ga kujera ka kwanta" juyawa ya yi yana neman kujerar, ta riƙe hannunsa, har kan kujerar. Ya hau ya kwanta a kai, ya na lumshe ido. Ta kalle shi ta ce "Idan ka sake shan kayan maye, sai na gaya wa 'yar madara, dan ka san ba ta mutu ta barka a kan wannan tafarkin ba" Ya ce "A'a Abla" "Idan ka kuma sha sai na gaya mata, duk ka ɓata mini rai ban ji daɗin ganinka a haka ba. Kamar ma na yi kuka wallahi" "Sorry ba zan sake ba in sha Allah" yayi maganar bacci nannauya ya na kwashe shi. Ta tashi ta koma kan teburinta, dan cin abinci, ta na yi ta na gudanar da aikinta, ƙarshe ta ture system ɗin ta kifa kanta ta hau bacci, domin daren jiya ba ta samu isasshen bacci ba, saboda ciwo. *** "Yaron nan ya fara bani tsoro, wai tambayata yake yi, in da P.A yake, ina tsoron kar na je ya san wani abu fa" "Indabo, ka kwantar da hankalinka, babu abin da ya sani, kuma babu abin da zai faru, kawai zunzurutun barazana ce" Indabo ya girgiza kai ya ce "Babu lallai barazana ce, shegen yaro ne fiye da yadda ka ke tunani. Ga waɗancan asararrun jarababbun yaran sun sako ni a gaba, yanzu Kanon nake son shiga amma har fargabar hakan nake ji, amma hakanan zan je na gano Abdul. Wallahi zaman prsion ɗin Jafar bai ɗaga mini hankali ba, kamar na Abdul. Gidajen yarin Nigeria da babu gyara, babu kula a haka yaron nan yake rayuwa, wai a haka an yi masa sassauci saboda wata banzar yarinya, kodayeke ko ma menene shi ne ya janyo wa kansa ai" Mutumin ya ce "Ka yi haƙuri distinguish, yaran namu ne ka haife su, amma ba ka haifi halinsu ba, kuma duk kankarofi ne kanwa uwar gami, tun da shi ne yake amfani da ƙarfin ikonsa, ya hana ruwa gudu ko ta ko ina" Cikin takaici Inadabo ya ce "Could you imagine Alhaji Sada, yaron nan kuɗin da ake tuhumar nan tawa a kai, ware su aka yi saboda campaign ɗin sa, amma saboda sakarci wai ya tattare kuɗin a kan tsinanniyar yarinya 'yar ƙauye, kuma hakan bai yi musu ba, sai da suka kai shi gidan yari, har da duka. Shi kansa alƙalin ba zan bar shi ba dan uwatar. Wani baƙin ciki da takaici da maimuna take gaya mini, wai yarinyar ciki ne da ita, ta cewa Abdul a zubar wai ba za a zubar ba, gaba ɗaya mutuncina da kimar siyasata ya zube, ban da Abdul ɗa na ne, da sai na yi masa aiken da babu dawowa. Amma ina nan ina shiri, Sai an kashe banzan yaron nan Viper, duk wata fitina shi ne yake ƙara kunnota. Gashi yarinyar nan 'yar jarida twins ɗin matarsa ce, daga rahotannin da na samu. Shiyasa farkon ganina da ita na tsorata, na saka aka yi mini bincike a kanta, amma gaba ɗaya nasabarta ba ta yi alaƙa da shi ko waccan matar ta sa da aka kashe ba. Saboda mugun rainin wayo, shi ma wancan wawan, wai ya na bincike amma a gidansu yarinyar na haɗuwa da Viper bai sani ba, shi ma sai na ɗauki mataki a kansa" Honorable Sada ya ce "Duk dai ka yi haƙuri ka kwantar da hankalinka, ai mun gama shirya komai, aiwatarwa ce ta rage. Kuma muna da tabbacin za a sami mafita" Indabo ya jinjina kai da alamar gamsuwa da maganganun honorable Sada. *** Barrister Habib ne ya shiga office ɗin Nabila, ya tarar da Viper a miƙe a kan kujera ya na bacci, Nabila kuma ta kifa kai ta a kan tebur ta na bacci. Gaba ɗaya sai ya ji babu daɗi, wani irin matsanancin kishi ya na taso masa, duk da ya san ko da me yake yawo, Viper ya fi ƙarfin yayi takara da shi, duk haryanzu bai gane in da suka dosa ba, daga ita har Vipern, amma kusancinsu yayi yawa. Ya ja da baya ya mayar da ƙofar ya rufe, ya na rufewa Viper kuma ya buɗe idonsa, ya bi ƙofar da kallo, ya mayar da idonsa kan Nabila da take baccinta a nutse, kamar ta samu gado. Ya daɗe ya na kallonta, sak 'yar madararsa yake gani, duk da akwai tarin banbancin halaye tsakanin Nabila da jauhar, amma akwai abubuwan ta da suke burge shi, she's very straightforward, very silly and arrogant. A hankali ya tashi ya kalli agogo, ya fice yaje ya yi salla, har ya dawo Nabila bacci take yi, kodayeke ba abin mamaki bane ba, ko lokacin da yana tare da jauhar, idan tana period kamar mai laulayin ciki, bacci ciye-ciye da saurin kuka. Ya daddaki teburin da ta kwantar da kanta, amma shiru ba ta motsa ba, "Ke wani daren za ayi miki ne?" Still ba ta motsa ba. Bayanta ya zagaya ya ja kujerar da take kai baya kamar za ta faɗi, razana tayi tare da yin wani ɗan marayan ihu. Ya ƙura mata ido ya ce "Ki tashi haka mu yi maganar da ta kawo ni" "Na ji amma ka ajiye ni mana kar na faɗi" A hankali ya mayar da kujerar, amma ya sunkuyo ta bayanta dai-dai kunnenta, kamar zai yi magana, sai kuma yayi shiru, ta din ga jin saukar numfashin sa a jikinta. Kame jikinta tayi, ta ce "Bari na wanke fuskata, sai mu yi maganar" ta tashi ta nufi toilet. Ta dawo ta zauna ta kalleshi ta ce "Ka watstsake?" Ya ɗaga mata gira. Ta ce "Alright, ina jin ka, meyafaru?" "Inadabo ya kira ni jiya, kuma tabbas tun da ya kira ni, akwai abin da ya taka yake jin ƙwarin gwiwa, har ya kira ni, amma menene shirinki ke yanzu?" Nabila ta jinjina kai ta ce "Alhamdilillah, dai-dai gwargwado muna da abin da ya sauwwaƙa, Bunkure na ta dragging ne to sai ta faɗi ɓarnar da ka aikata a baya" "Nabila ba fa zan koma prison ba" yayi maganar very serious. Ta waro ido, sai kuma ta ɓata fuska "Nabila kuma garangatsau ba Ablan" "Am very serious, kin san masifar gidan yari, ba fa zan koma ba" Nabila ta ce "Easy, in sha Allah ba abin da zai mayar da kai prsion, amma Vi" Ya kalleta. Ta kwantar da murya ta ce "Ina ganin yakamata mu fara zuwa kana ganin likitan ƙwaƙwalwa sab... Haɗiye maganar ta yi, saboda ganin kallon da ya yi mata. "Kallon mahaukaci ki ke yi mini kenan?" Da sauri ta girgiza kai ta ce "No, ba kallon mahaukaci nake yi maka ba, za su taimaka maka ne, ka daina ta'amalli da kayan maye gaba ɗaya, tun da ka na trying kai ma, za su taimaka maka, zuwa wurin likitan ƙwaƙwalwa ba ya na nufin mutum ya haukace bane ba". Shiru ya yi yana kallonta. "Please Vi, kar ka ce A'a zaka iya daina shaye-shaye gabaki ɗaya, idan muka dage da zuwa wurin likitoci, dan Allah kar ka ce A'a ka ji" "Ba zani ba" "Dan girman Allah, kar ka yi mini haka ka taimaka dan Allah, ka ji Vi, na jinjinawa ƙoƙarin da ka yi, na rage kaso mafi rinjaye a shaye-shaye, amma za su taimaka maka, dan Allah ka yarda mu je" Tashi ya yi tsaye, ya ce "Tashi mu tafi" ba ta sake yi masa maganar ba, suka tafi. **** Sanarwa ce ta fita, na ɓatan P.A ɗin Indabo, nan da nan da taimakon Sumayya, da murtala, aka cigaba da yaɗa ɓatan nasa babu ƙaƙƙautawa, kamar yadda Viper ya nemi su yi hakan, ta hannun Nabila. A yau ma kotun a cike take da ɗan Adam, domin kuwa daga cikin shari'un da suke ɗaukar hankali, har da ta Amini Viper. Viper ya zama shaida na ƙarshe da Nabila za ta gabatar wa kotu. Ya fito ya tsaya, Nabila ta tsaya a gabansa, ta jinjina masa kai alamar ƙwarin gwiwa. Ta numfasa ta ce "Malam Al'amin, ko zaka iya bayyana wa kotu, abin da ya faru a ranar da ka ke zargin waɗan nan mutanen da shiga gidanka, su kashe maka mata" Tana kai maganar ya tari numfashinta da "Ba zargi nake yi ba na tabattar" "To meyafaru?" Ya yi ajiyar zuciya ya ce "Ina kwance na fara jin motsi a saman katanga, na taso na fito falo, aka haske ni da fitila. Na tambayi waye, ba na iya gane suwaye, sai gilmawar mutane, na ji an daki ƙafafuwana da wani abu mai nauyi. Kafin na yinƙura, na ji tsinin allura a wuyana, na yinƙura zan kuma tashi, aka daki ƙafafuwana, suka daddane ni, su ka ɗaure mini hannayena da ƙafafuwana. A lokacin Madaki ya sauke takunkunmin fuskarsa, da shi da lakwari, na kasa motsi, gaɓoɓina su ka fara sanyi. Idona biyu amma na kasa motsa ko ina a jikina, a dai-dai lokacin matata jauhar ta fito. Bayan yi musu magiyar su rabu da ni, Madaki... Sai kuma ya yi shiru, ya na haɗiyar yawu. Nabila ta jinjina masa kai alamar ya cigaba. Lakwari ya riƙe gashin kanta, Madaki ya hankaɗata, Madaki kuma ya sanya mata ƙafarsa, ta faɗo a kan cikinta. Su ka buga mini a kaina daga nan ban sake sanin meyafaru ba. Ya ƙarasa maganar a sanyaye. "Ka tabattar ka ga mutuwar jauhar?" Ya jinjina kai alamar eh. Nabila ta kalli alaƙali ta ce "Ina fatan wannan kotu mai adalci, za ta yi duba da shaidu da hujjojin da mu ka gabatar, ta tabbatar da adalci wurin hukunta ma su laifi" Aka waiwayi bunkure, kan ko ta na da abin cewa, ta tashi ta ta ce ta na da tambayoyi ds za ta yi wa Viper. Ta zo gabansa ta tsaya, ta kalleshi ya kalle ta, ta yi murmushi ta ce "Al'amin, binciken jami'an tsaro da ya gabata a kan kisan matarka, sun tabbatar da cewa, kai ka sha kayan maye, ka halakka matarka da hannunka, amma sai gashi ka na zargin wasu da shiga gidanka su ka kashe matarka" Ta sake kallonsa a tsanake ta ce "Ka na ta'amalli da miyagun ƙwayoyi, eh ko a'a?" Viper ya yi shiru ya na bin idonta da kallo. Nabila ta nemi a dakatar da Bunkure, saboda ƙoƙarin sanya Viper amsa laifi ta ƙarfin tsiya, sai dai ba a karɓi ƙorafin ba, aka ce ga ci gaba. "Ko ba ka amsa da bakin ka ba, amsar eh ce.Ya mai girma mai shari'a duniya kowa ya shaida Al'amin Viper ko in ce mai zamani, gawurtaccen ɗan daba ne da ya gagari al'umma, har a bayan tserewarsa daga gidan yari, ya ci gaba da aikata miyagun ayyukansa, na sara suka da dillancin miyagun ƙwayoyi". "Objection my lord, barrister Naja'atu ta na kare waɗanda ake zargi ne, ko kuma ɗorawa mai ƙara laifuka da hanyar karkatar da shari'ar kan wani abu daban". Aka gargadi Naja'atu Bunkure, ta ɗaukko wani file ta ɗaga ta ce "A bincike da yan sanda su ka tattara, akwai binciken likitoci, da gwaje-gwajen da aka yi masa bayan mutuwar jauhar, wanda a jininsa aka gano sinadarin wata allura, da ake amfani da ita a asibiti, wadda sai da matakai masu tsauri ake amfani da ita. Bayan haka akwai sauran ƙwayoyin da aka gano sinadaransu a cikin jininsa, wanda hakan yake tabattar da shi ya sha ya bugu, ya kashe matarsa da kansa. Da wannan nake roƙon kotu ta wanke waɗanda ake zargi, a hukunta wanda ya aikata laifin" Tsit kotun tayi, wani irin gumi ya tsatstsafo wa Viper, ba shi ba hatta su Walid, sun shiga cikin matsanancin tsoro da fargaba, ga su Abbu da mama hatta Alhaji mu'azzam da duk wani majiɓancin shari'ar, suka shiga cikin damuwa da tashin hankali. Nabila ta kalli Bunkure, Bunkure ta kalli Nabila tana murmushi. Nabila ta ce "Zan so kotu ta banu dama, na gabatar da doctor Muktar sharfaɗi" Aka ba ta dama, sak Viper ya yi, ya na tunanin shi kuma me doctor Muktar zai yi a nan. "Doctor ka gabatarwa da kotu kanka" "Sunana doctor muktar sharfaɗi, ni ne likitan da na duba marigayiyya jauhar, na tabattar da inducing ɗin ta za a yi a asibitina, kuma ni aka samu na tabattar da mutuwarta a asibitin gwamanti na shiga asibitin safe. A report ɗin da na bayar, babu duka a jikinta ko kaɗan, faɗuwa ce, ta rasu ɗan cikinta ma ya mutu. Sai dai zan yi wani karambani, ban san wane irin bincike barrister ta yi akan allurar da take magana a kai ba, wannan allura ta na fara aiki ne mintuna biyar zuwa bakwai da yin ta, kuma tana tafiyar da ji da gani da consicous ɗin mutum gaba ɗaya, babu yadda za ayi wanda ya yi amfani da wannan magungunan ko alluran, ya iya sanin meyake yi, har ta kai ga ya yi kisan kai, kashe jiki suke yi gaba ɗaya Banbancin mutum da matacce numfashi ne kawai" Nabila ta numfasa, ta je gaban teburinta, ta ɗaukko wata envelope ta fito da wasu hotuna, ta ɗaga su ta ce "Mai girma mai shari'a, waɗannan su ne hotunan farko da jami'an tsaro su ka ɗauka, bayan ƙorafin da maƙwabta su ka shigar, na cewar sun ji ihun jauhar cikin dare, wayewar gari kuma sun yi ta bugu ba a buɗe gidan ba. Idan aka yi duba da hotunan, Al'amin kwanciyar da yayi ruf da ciki, hannayensa a kan gadon bayansa, ya na nuni da cewa tabbas ɗaure shi aka yi. A wannan hoton kuma, idan aka duba wurin ƙafafuwansa kasancewar ba dogon wando ne a jikinsa ba, akwai shaidar an yi traumatizing wurin, akwai alamar shaidar ɗauri a wurin. Idan har binciken jami'an tsaro dai-dai ne, kamar yadda Barrister Naja'atu ta faɗa, to ya tabatta toxicating ɗin Al'amin aka yi aka kashe matarsa. Idan kuwa har shi ne ya kasheta, zai iya zama tsautsayi ne, dan idan niyyar kasheta ya yi, zai daketa ne, ko jikinta ya nuna wani nau'i na cutarwa. Amma daga bayanan doctor Muktar, da hotunan da na gabatar, ina fatan Al'amin ya fita daga zargi, kuma za ta hukunta waɗanda suka aikata laifin" Da ido kawai Viper ya din ga bin Nabila, dan bai san yadda aka yi duk ta tattara waɗannan shaidun da hujjojin ba, sai a yanzu ya ƙara jinjinawa basirarta da hangen nesa. Alƙali ya yi rubuce-rubuce Alƙali ya ɗauki lokaci ya na yi, daga baya ya ce ya sake ɗaga shari'ar zuwa wata guda, domin yin zama na ƙarshe domin yanke hukunci. Kamar wata celebrity, haka Nabila ta fito daga cikin kotun, su Abba suka kewaye ta, kowa ya na tofa albarkacin bakinsa, su na jinjina wa ƙoƙarin da ta yi. Viper gefe ya koma ya tsaya ya na kallonta, yadda farinciki ya mamaye fuskarta. Sumayya ta saka mata abin magana, ta na tambayarta, yaya take ganin gudanawar shari'ar. "Babu abin da zamu cewa Allah sai godiya, muna sanya ran samun adalci,  a wannan shari'ar". Hatta su liti ma, kasa ɓoye farincikin su su ka yi. Viper bai tsaya ba, yau ma saboda Abbu ya na wurin, ba ya son duk abin da zai haɗa shi da shi. Daga nan duk su ka watse, Baba ya na ta son lallaɓa Nabila ta dawo wurinsa, amma yadda ta nuna ba ta so, ya sanya ya ƙyaleta. "Thank you very much, for standing by my side, and show me way, to live another life as a different person, a really appreciate Abla, thank you once again take care. Al'amin" Murmushi ne ya suɓuce mata, sai kuma ta ɗan tsuke fuska a hankali ta furta "Alaƙarmu za ta zo ƙarshe, da zarar na kammala wannan shari'ar" Ayshercool 08081012143 95 Duk da abin da ta ƙudurce a ranta, amma ta karanta message ɗin nan, ya fi sau ashirin. Haryanzu tana tantama a kan hukuncin da ta ɗauka, na rabuwa da shi da zarar ta kammala shari'a, amma itakaɗaice mafita a ganinta, saboda ta na ganin soyayya da Viper tamkar cin amanar 'yar uwatta ne, babban abin da za ta yi, a matsayin ba ta santa ba, shi ne ta tabbatar da an ƙwato mata hakkinta, kuma an wanke Viper daga zargi. Viper kuwa su na tafe, Liti ya yi wani irin ihu, ya ce "Kan uban nan, yarinyar nan ta yi bala'i, ashe haka kanta yake ɗaukar wuta, kamar me. Kai ka ga wata karakaina da shige da fice da ta yi, ashe ta san abin da take yi" Ɗan mama ya ce "Oga liti, ka manta lokacin da ka din ga korarta, Allah ne ya sa Oga walid bai yi saurin korarta ba, ya bari ta ci gaba da zuwa, ina ga a wannan gaɓar babban yaya za mu sarawa, Mikiya mai hangen nesa, amanar Oga Viper kuma babban yayan marigayiyya, an buga da kai an barka" Walid ya yi murmushi, ya ce "lokuta da dama, abin da haƙuri bai bayar ba, akasinsa ba ya bayarwa. Kai yanzu da mun koreta, da idan Allah ya ƙaddara za ta tsaya masa, sai mun je mun nemota, idan kuma lauya zamu ɗaukar masa babu lallai mu samu yaƙinin ba za a saye shi da kuɗi ba ya cutar da mu ba. Wallahi hardwoker ce Nabila, gashi babban abin da yake burgeni da ita da Jauhar, sun iya kwantar da kai, su yi galaba a kan abu, Nabila ba ta da tsoro da ni wani ne, sai na karrama yarinyar nan. Kuma kai yanzu ka ji kunya, irin abin da ka din ga yi mata" Liti ya ce "Na ji ɗin, amma duk da haka ai ba ta da kunya muguwar fitsararirriya ce" "Liti ka daina rinjayar da laifukan mutum a kan alkhairin sa mana, kowane ɗan Adam tara yake bai cika goma ba. Ita jauhar ɗin ce maka aka yi ba ta tsiwa, ka tambaye shi ka ji to, ba ta yi wa kowa amma ta na yi masa, ko ƙarya nayi?" Yayi maganar yana kallon Viper. Viper ya yi murmushi ya na tuna yadda ya sha jifa da kwanuka a hannun Jauhar. Nabila kai tsaye take abubuwan ta, babu ɓoye-ɓoye ko kara, Jauhar kuwa cikin ruwan sanyi, a ɓoye take ladabtar da shi. Walid ya ce "Ko ma yaya ne, ni Jauhar tawa ce, Nabila ma haka, kowacce ta taimaki rayuwarmu. Ba dan Allah ya kawo Nabila ba, da tuni mai zamani ya samu taɓin hankali, ko kuma ya kashe kansa, kalli yadda muka din ga fama da shi, saboda yi wa kansa allurai. Amma tana faɗowa rayuwarsa, ta saita shi, kai ba iya lauya ba ce ba, har role ɗin likita tayi playing, kalli multiple attempts na kasheta, da intimidation da ta din ga fuskanta, amma ta dage ta jure, ko yau ta barka, ta biya Jauhar ina yin ta sosai, ina yi mata fatan iyayenta su samu fahimtar juna, ita ma ta samu nutsuwa, a zo ayi bikinku mu huta" yayi maganar yana kallon Viper da bai ce uffan ba. Liti ya ce "Ba wani nan, ba fa zai sake yin aure ba, kawai ya haƙura ya shiga ittikafi da yi wa addini hidima har ƙarshen rayuwarsa, saboda wani takaici nake ji, idan na ji an yi zancensa da wata ba jauhar ba. Dama ba damuwa yayi da wata sabgar mata ba, zai iya lallaɓa rayuwarsa a haka, ko mai girma Al'amin" Kawar da kai Viper ya yi yana dariya, iya shege ɗan liti yake ji, wai ya shiga ittikafi. *** Yau aka ɗaukko ɗan uwan ramma Sani daga makarantar kwana da yake yi a Dutse, kamar su haɗiye juna da shi da ramma. Ya ce "Yaya na kasa gane yaya ki ke ma, rama ki ka yi ko ƙiba, kin wani goge, ashe zan ƙara ganinki, nayi kuka sosai har na fid da ran sake ganinka ma" Tayi murmushi ta ce "Nayi kewarka sosai da sosai da kai da mama, na yi kuka iya yi na, ban taɓa zaton zan sake ganinku ba, amma Alhamdilillah ala kulli halin, ya makarantar?" "Lafiya ƙalau, ni fa kusan shekara ban dawo kano ba, idan an yi hutu a gidan wani abokin honorable nake zama, wanda ya saka aka kawo mu nan aka ajiye, wannan karon na saka aka roƙe shi tun da an ce mini an ganki, kin ga kayan alatun da ake bani ramma, A dalilinki kalli daɗin da muke ciki, da muna ƙauye muna fama har da cin dafaffiyar tafasa mun sha wahala sosai" ramma tayi murmushin yaƙe. "Yaya bayan tafiyarki fa, kin ga kwaltar da aka shimfiɗa, tun daga tasha har cikin tofa an yi tituna aka gyara makarantu, amma dai kin je ƙauye ko da ki ka fito, kamar yan birni, har da fitilun sololi aka saka mana, ga ruwa" Ramma ta girgiza kai ta ce "Ban je ba, tun da na fito ina nan" Suka din ga hira da ita. Dawowar Sani, ba ƙaramin daɗi ta yi wa ramma ba, sosai yake zama su yi hira ya saurareta, saɓanin mama da yanzu sama-sama take da ita. Shi dai tun yana kallon ramma, yana mazewa har ya magantu ya ce "Yaya wai aure ki ka yi ne da gaske, kamar yadda kawunmu ya ce ya aurra da ke?" Ta kalleshi ta ce "Me ka gani?" "Gani na yi kin kusa haihuwa" ya bata amsar da ta kusa sanyata nutsewa, yanzu duk ɓoye-ɓoyen nan da take yi, sai da Sani ya ga cikin nan. Ta ce "Eh da gaske ne" "Ikon Allah, to ina mijin naki yake, ni gaskiya ban so yayi miki irin wannan auren ba, na ci buri da yawa a kan aurenki" Ramma ta katse hirar, ta ce masa za ta je ta kwanta, bacci take ji. Ta je ta haye kan gado ta kwanta, ta din ga kallon ɗakin, duk albarkacin abin da ya faru da ita ne, ta samu wannan ni'imar, da tana rayuwa a ƙasƙance cikin talauci, amma yanzu tana cikin ni'ima duk da ƙaddarar da ta kawota wannan bugiren ba irin wadda ake fata ba ce. Ta ji yadda abin da yake cikinta yake motsawa, ta shafi cikin a hankali, tana tunanin Abdul. Da tunanin halin da yake ciki yanzu, ko ciwonsa ya warke Allah masanin gaibu, dan ba ta da wata hanya ta ganinsa, idan ba Nabila ce ta wayance da kaita awo, ta kaita wurinsa ba. *** Nabila ta halarci program ɗin su, da su ka saba yi da Sumayya, Sumayya ta din ga yi mata tambayoyi a kan shari'ar da take gudanarwa ta Viper, nan Nabila ta din ga fito da wasu bayanai da mutane da yawa ba su san da su ba, iya abubuwan da suka ji a kan sa a bakin Mutanen gari, da na jamu'an tsaro kawai da shi suke amfani su yi masa hukunci. Har tarihin yadda ya shiga daba a dalilin kisan ɗan uwansa da rashin ɗaukar mataki, sai da ta bayar, duk da ta ɓoye duk wani abu da ya shafi familynsa. Abbu yana tafe a mota, yana driving yake sauraren shirin, sai tsananin mamakin abun ya kama shi, mussman ɓangaren shekara biyar da ya yi a prsion, ba tare da an yi masa shri'ar ba, aka sake shi, kuma aka koma wai ana nemansa wai an sake shi ba bisa ƙa'ida ba. To zaman me ya yi na shekara biyar ba ayi masa shari'a, a ƙaddara yanzu a yanke masa hukuncin laifinsa, da lissafin waccan shekara biyar ɗin za ayi, ko banda ita? Haka ya tafi gida, ya na ta lissafi daban daban a cikin zuciyarsa. Ji yayi kamar ya nemi Nabila, amma sai ya rabu da ita, gaba ɗaya topics ɗin da suka yi discussing sun ɗauki hankalinsa sosai da sosai, tare da mamakin yadda fannin shari'a da tsaro ya lalace ya taɓarɓare da cin hanci da rashawa, kawai wa ka sani waye ya sanka. Maganganunta suka ci gaba da ɗaukar hankalinsa, da take kira ga iyaye, da al'umma da hukumomi su guji watsi da yaransu dan suna rashin ji, idan yaro yayi laifi, iyaye su bar hukuma ta hukunta shi, idan an sako shi, su rungumi abin su, su ci-gaba da addu'a da yi musu nasiha, ta din ga bankaɗo illar da watsar da yaron da ba ya ji da iyaye suke yi, a waje kuma su samu mai rungumar su, komai munin halinsa dole su yi masa biyayya. Gaba ɗaya Abba bai taɓa tsammanin Nabila ta na da hankalin da za ta yi bayanai masu muhimmanci har haka ba. Jikin Nasir ya fara sanyi, mussman yadda ya ga ko ina zancen Nabila ake yi, da yadda shari'a ta fara karkata, ƙoƙarin haifar da abin da bai yi tsammani ba. Abba ya samu Nasir a gida, ya ce "Nasiru, ka ji program ɗin Arfa kuwa?" Ya ce "A'a Abba, meyafaru?" "Maganar yaron nan ɗan daba da ta ƙallafa ran kare shi, alamu fa sun nuna kamar yana da gaskiya. Koma dai ba shi da gaskiya, akwai zalunci a cikin abin da aka yi masa". Nasir ya ce "Haka ne, amma duk da haka mu jira a kai ƙarshen shari'ar, tun da yana da iyayen gida, maybe akwai masu tallafa musu har da Nabilan a kan shari'ar" Abba ya ce "Haka ne, amma duk da haka, ɓangarorin shari'a a ƙasar nan da gyara, yaya za ayi a ajiye mutum shekara biyar babu Shari'a, to zaman meyake yi ba a yanke masa hukunci ba? Kai Allah ya kyauta" duk jikin Nasir ya bi yayi sanyi. ***** Viper yana ta son ya kira Nabila, amma bai san me zai ce mata idan ya kirata ba, dan haka ya din ga jujjuya wayar, yana kallon lambarta. Babu tsammani, ya kalli liti ya ce "Abdallah" "Na'am mai zamani" "Yaushe rabonka da gida ne?" Jin tambayar yayi wani iri, "Kusan shekara ɗaya da rabi" "Yakamata ka je ka gaishe su, mussaman kai da iyayenka suke a raye, ba kamar ni da Walid ba". Liti ya ce "Kai ma ai Abbu yana da rai" "Ina magana kana mayar mini?" Viper yayi maganar yana tsuke fuska. "Easy maza, ni wallahi wannan munafukar tsohuwar ce ta saka na daina zuwa gidan, tayi ta hantarata tana ziga Alhajinmu, shi ma fa korata yayi, maminmu na kallo, ba ta ce komai ba. Ai ni da gidan nan idan ba wannan algungumar tsohuwar ce ta baje tayi bacci ba, gaskiya na daina zuwa, ga tsinuwa da take yi mini, dan ma Allah ya sa Alhaji ta haifa ba ni ba, da sai na kwashe ƙasusuwan ƙafarta na watsar da ita" "Yakamata mu buɗe wani sabon babi na rayuwa ne Abdullahi, mu gyara wasu daga cikin kura-kurai waɗanda za su iya gyaruwa, akwai yiwuwar idan mu ka yi nasara a kotu, na koma can kudu da aiki, koma na bar ƙasar gaba ɗaya, ba zan taɓa tafiya na bar ku ba tare da wani ƙwaƙwƙwaran madogara ba" Walid da tun ɗazu yake wanki bai ce komai ba, ya ce "Aikin me ka ke yi wai? Kuma meyasa zaka tafi kudun?" Viper ya yi murmushi ya ce "Zan yi muku bayani a gaba, amma dole muje ka gaida iyayenka, ka ba su haƙuri liti" "Dan Allah maza ka bar zancen nan, nima fa yakamata su nemi yafiyata fa, mussman algungumar tsohuwar nan" "Ba zaka daina ce mata algungumar nan ba ko?" Liti ya ce "Saboda fa Alhaji ya yi mata biyayya ta saka ya kore ni, wai zan lalata mata sauran jikoki, lokacin ma fa ba wani nisa nayi a shaye-shaye ba, amma wani ƙanin babanmu ya ce wai alhakin yaransu ne, da babanmu bai haɗa da su, ya kai ƙasar waje karatu ba, shegu kamar su suke tara masa kuɗin. Ni Allah yasa ma ba asiri suka yi mini na je na dawo ban iya komai ba, sai holewa" Walid ya ce "Ko ba komai, ai ka hau jirgi" Liti ya kwashe da dariya ya ce "A banza amma" Ɗan mama ne ya faɗo cikin gidan, suka kalle shi gaba ɗaya, liti ya ce "Menene kuma?" Yayi tsuru-tsuru yana kallonsu. "Kai dalla menene wai?" Ya numfasa ya ce "An kashe brothern Viper, wannan na gidan na su Abba" sai da Viper ya zabura, ya kalli Ɗan mama ya ce "What? How?" Ɗan mama ya ɗan girgiza kai ya ce "Faɗa su ka yi da wasu a can unguwar bello wai a kan kare, shi ne suka ƙyale shi, sai da ya dawo daga yawon cajinsa, suka sassara shi, suka saka shi a buhu, suka kai shi gefen Black ocean kududdufin nan na cikin unguwa suka watsar. Ashe kwana uku ana nemansa ba a ganshi ba" Miƙewa Viper ya yi, jikinsa yana tsuma, kamar zai fita daga hayyacinsa ya ce "Yaushe ya fara shaye-shaye har yake bin yara marasa ji? Kuma jiya a kotu, ban ga alamar akwai Matsala a tare da Abbu ba" Ɗan mama ya ce "Taɓ ai an kwana biyu, yana zuwa rumfar shayinmu, wurin su ɗan kada ai, yana shaye-shaye". Takalmansa ya shura zai fita, cikin matsanancin tashin hankali, Walid ya riƙe shi, ya ce "Ina zaka je?" "Meye haka, cika ni mana na je na ji meyake faruwa? Kuma suwaye suka yi masa wannan zaluncin" Walid ya ce "Babu in da zaka je, a sabga irin tamu, duk wani ɗan gang, ya san irin haka na iya faruwa da shi, muddin bai tuna ba, ko ma mutum ya tuba, ko a kashe ne ko kuma a kashe shi" "Walid, Abba ba zai iya daba ba, ina ganin shaye-shaye kawai yake yi, wane irin kisan zalunci ne wannan da rashin imani? A sassara mutum a zuba a buhu aje a zubar?" Liti ya ce "Ni ku matsa mini, na yi sujudar godiya ga Allah, gabasa ake kallo ko daga nan Arewa ma zan iya yin ta? Daɗina da kai wasu lokutan kana da wani ɓoyayyen rauni, da ya kan kusa cutar da kai Viper. Matar da ta rufe muku ƙofa, aka hallaka ɗan uwanka, shekarun da suka gabata, sharrin da ta aika ne, ya dawo mata kanta a kan ɗanta ita ma, cin amanar da ta yi, ita ma Allah ya ɗanɗana mata, Allah Allah ne, dan haka babu ruwanka". "Liti kai mahaukaci ne? Ko kaza aka kashe wa mutum bisa zalunci, abin tashin hankali ne, mai rai a sassara shi, a saka a buhu, a kai a yar fa" Walid ya ce "Yanzu idan ka je gidan me zaka yi musu? Salon ta ce kai ne ma ka saka aka kashe shi, ka san halinta ai, babu in da zaka je, taje Allah ne ya kamata". Fafur suka hana Viper fita, ya koma cikin ɗaki, ya ɗaukki wayarsa ya kira Nabila. Ta ɗaga tayi sallama ta ce "Vi ya ne?" "Amm ki tambayi ƙawar nan taki Sumayya, ko labarin kisan da aka yi wa wani yaro Abba a unguwarmu, ya je mata dan Allah ina son a ɗan bikcika". Ta ce "Subhanallah, ban sani ba, bari na kirata na ji" "Yauwwa yi sauri, dan Allah idan gaske ne, Joseph ya kai ku station ɗin da case ɗin yake hannunsu, ku jiyo mini ya ake ciki?" Ta ce "An gama ranka ya daɗe, amma ya sunan wanda aka kashe ɗin?" "Ɗan matar Abbu ne, sunansa Abba idan ya kama ku je gidanmu, ku ƙara tabattar mini". Mamki ya cika Nabila, amma ta ɓoye mamakin nata ta ce "In sha Allah zamu je" ya katse wayar cikin matsanancin jimami. Walid ya ce "To wai meye amfanin hakan da ka yi? Meye naka a ciki Viper?" Al'amin ya girgiza kai ya ce "Yaya ku ke abu kamar ba tsoffin 'yan hannu ba? Yanzu faɗan ɗaukar fansa zai ɓarke a tsakanin unguwannin, kuma ina gudun abin da ya faru da ni, ya sake faruwa a kan wani, ina son na bibiyi abin a kama waɗanda suka kashe shi, na tabattar da an hukunta su, domin ya zama izina. Kuma ko ba komai, musulmi ne, kuma mahaifina ne ya riƙe shi, an yi masa kisa mai muni, abin da taɓa zuciya" Sai kuma suka yi shiru, liti ya ce "Haka ne, maganarka dutse, amma gaskiya ba zaka je ba, ba ruwanka daga nan kayi masa addu'a, idan komai ya lafa sai a san abin yi" Viper ya ja tsaki, tare da girgiza kai. Walid ya ce "Menene kuma?" Yayi ajiyar zuciya ya ce "Walid, babu wani alfanu ko jin daɗi a rayuwar daba da shaye-shaye, duk kalle mu dai, babu wanda wannan rayuwar ta amfana da komai, face tabon baƙin ciki da tsantsar nadama. Akwai tarin ƙalubale, muddin za a ci gaba da tafiya a haka" Walid ya ce "Haka ne, sai fatan Ubangiji Allah ya yafe mana ya shiryar da mu baki ɗaya". Kamar yadda Viper ya buƙata, Nabila tare da Sumayya, suka tafi binciken da ya ce, jami'an tsaro suka tabbatar da faruwar Al'amarin. Sumayya ta je har gidan su Viper, kamar sai dai ba su tafi tare da Nabila ba. A rumfar zaman makoki, ta hangi Abbu, ta ƙarasa tayi musu gaisuwa, Abbu ya taso, suka sake gaisawa, ya ce "Sumayya ya aka yi ne?" "Nabila ce ta kirani, Viper ya ce lallai mu zo a tabattar da abin da ya faru, ban san dai dalilinsa na yin hakan ba" Ya ɗan yi shiru ya ce "Shi da kansa?" Ta ce "Eh" nan ya sake yi mata bayanin abin da ya faru, maganar da yake yi mata ma, mahaifiyarsa na Asibiti allurar bacci kawai ake yi mata, tamkar zata haukace, saboda yadda aka kawo gawar Baba, jikinsa ya fara zagwanyewa, jikinsa ko ina sara, hannunsa ma daban aka kawo shi. Sumayya ta tattara rahoton abin da ta samu, ta sanarwa Nabila, kuma ta samu na sanarwa a gidan rediyo. Sosai batun ya ɗauki hankalin jama'a, Duk ita kanta Nabila, sai da ta ce Alhakin Viper ne, amma ta kaɗu matuƙa jin irin kisan tozarcin da aka yi wa Abban duk a silar ƙwaya. Kamar yadda ta wallafa a shafinta, suna nan suna zuba ido, su ga matakin da jami'an tsaro za su ɗauka, wurin cafke waɗanda suka aikata laifin. **** Rahila dai abin da ya samu Abba ya zame mata masifa, ta daina magana ta daina cin abinci, ba ta gane kowa sai kuka, idan aka jima kuma ta yi ta kurma ihu, tana kururwa tana kiran ɗana Abba, Abba bai mutu ba, sai dai a daddaneta ayi ta yi mata allurar bacci. Haka Shahida zata rungumeta, tayi ta kuka, ga Amira ta shilla ta yi nata wuri, tun da Abbu ya ce ba zai karɓeta a gidansa ba. ***** Yau da yamma Viper ya je barrack wurin Nabila, sai dai tun kafin yayi magana, ta fuskanci matsananciyar damuwa a tattare da shi. Ta ce "Vi meyafaru ne?" "Abin da ya faru da yaron nan Abba ne ya yi bala'in tsaya mini Abla" "To yaya za ayi, sai addu'a, amma in ganin kamar har da hakkinka abin da ya same su" Viper ya girgiza kai ya ce "Ba na tunanin haka, haka kurum abin ya tsaye mini. Shikenan dai makomar ɗan shaye-shaye ko ɗan daba. Ko ka kashe ko a kasheka, ko a kashe maka wani makusancinka, da zai bar maka mummunan tabo a zuciya, babu riba sam a wannan harkar". Ta gyaɗa kai ta ce "wannan haka yake, amma ka godewa Allah da ya sanya ka farga da wuri, har ka ke ta ƙoƙarin tuba ga Allah, ina fatan Allah ya karɓi tubanka" Ya amsa da "Amin ya Allah, kuma kema ina yi miki godiya sosai Abla, kema kin bayar da gudummawa sosai da sosai a cikin rayuwata, kamar yadda sisternki jauhar ta yi mini, Allah ya saka muku da mafificin alkhairi" Tayi murmushi ta amsa da Amin, duk wannan basar da abubuwan da yake yi, ashe yane sane da duk alkhairin da ake yi masa. "Amm ya maganarmu ta zuwa asibiti, me ka yanke a kai?" Ya jinjina kai ya ce "Zani in sha Allah" Faɗaɗa murmushinta ta yi, ta ce "Alhamdilillah ala kulli halin, amma na yi murna na ji daɗi sosai da sosai, Allah ya tabattar da alkhairi" "Amin" "To menene next, idan an kammala shari'a, sannan ya zamu yi da batun indabo? Shi Shikenan ya ci bulus kenan, idan aka hukunta su madaki shikenan?" Al'amin ya haɗiyi yawu, ya ce "Shi wannan iya jarrabawar da yake ciki ta ishe shi, ko iya yanzu ya san tasa ta ƙare, akwai jarrabawa a rashin mulki, tarwatsewar iyali kamar yadda na fuskanta. Bore daga magoya baya ga karayar arziki an kama kayansa a ƙasar waje da yaransa, ga tuhuma da yake fuskanta a cikin gida da sauransu, bana buƙatar wani ya hukunta indabo ni ne zan hukunta shi" Ta waro ido ta ce "Dan girman Allah mun kusa zuwa gaɓar ƙarshe, kar ka mayar da mu baya ka ɓallo mana wani babban aikin dan Allah". "Haba akwai bambanci tsakanin Al'amin ɗan daba da kuma jami'in tsaro, na san abin da nake yi, ki kwantar da hankalinki" Nabila ta ce "Anya kwanciyar hankalin nan kuwa?" "Trust me mana" yayi maganar yana murmushi. Ranar Litinin, Nabila da Viper da rakiyar Sumayya, suka kai Viper Asibitin ƙwaƙwalwa, domin ya ga likita. Ba su wani sha wahala ba, ya samu dukkanin kulawar da yake buƙata, hatta history na yadda ya fara shaye-shaye, sai da suka yi wa likitan bayani, aka tura shi yin wasu gwaje-gwaje. **** Kwanaki suka ci gaba da shuɗewa, wasu daɗi wasu akasin haka, ana tsaka da alhinin mummunan kisan gillar da aka yi wa Abba, Rahila ba ta gama dawowa dai-dai ba, aka sake sanar da ita, an kama Nazifi a Lagos, tare da manyan 'yan fashi, hakan ya ƙara tunzura nutsuwar ƙwaƙwalwarta. Kwanci tashi asarar mai rai, aka sake shafe watanni guda curr, Ramma kullum cikin lissafi take, yaushe Abdul zai fito daga tsaren da yake. Yau kotu ta fi ko yaushe cika, ana jiran hukuncin da kotun zata yanke. Ƙarar su Viper ce ta uku da aka kira, bayan dogon rubuce-rubuce da Alƙali ya yi, da bayanai ya shiga karanto hukuncin da za a yanke wa su Lakwari. Shekarun ɗaurin rai da rai, kowannensu, sannan kotu ta yi umarnin a cigaba da binciken in da sauran waɗanda su ka tafka ta'asar tare suke. Wata irin ajiyar zuciya Nabila ta sauke, hawaye suka din ga zuba daga idanunta, ba zata taɓa manta wannan rana ba, domin kuwa wannan ita ce mafi ƙololuwar nasara da ta samu. Viper ma sunkuyar da kansa ya yi a wurin, hawaye ya kasa barin idanunsa, duk da Madaki yana can gadon Asibiti, bai san ma waye a kansa ba. Ana gama yanke hukuncin ta yi waje, da Sumayya ta fara arba, suka rungume juna, Nabilan sai kukan farinciki take yi. 'yan jarida ne suka baibaiye ta, suna yi mata tambayoyi, amma Sumayya ta ce su ƙyaleta ba ta cikin nutsuwarta. Walid ne ya fito tare da Viper, yana ta rufe fuska da handkerchief, babu abin da yake iya sanya shi hawaye a take, sai tuna jauhar, 'yan jarida shi ma suka yo kansa, amma ya rufe fuskarsa, Liti ya ce "Ko me zaku tambaya ku tambayeni, ba zai iya magana ba" "A'a da shi muke son yin magana" "To ba zai yi ba, munafukai kamar baku ku ka din ga zuzuta lamarin baz da faɗar ƙarya da gaskiya, wallahi idan ba ku bi a hankali ba, sai aikin nan ya kai ku wuta, saboda yaɗa fasadi da sharrin da k... "Kai liti wai waye ya tambayeka ne?" Walid ya dakatar da shi. Baba yana tsaka da rarrashin Nabila, ta daina kukan da take yi, ya ga Viper ya fito, ya nufe shi, yana zuwa ya rungume shi ya na "Ina tayaka murna Aminullahi, Ubangiji Allah ya wankeka yau, ni dama na faɗa ba zaka iya kashe mini jauhar ba, Allah ya yi maka albarka". Abbu yayi tsuru daga gefe, yana son yin magana, amma ya kasa wata irin kunya ta mamaye shi. Alhaji mu'azzam ma gefe ya koma yana murmushi, amma bai tunkari in da Viper yake ba. Viper ne da kansa ya tunkari in da yake tsaye, ya je gabansa ya miƙa masa hannun sa. Sai da Alhaji mu'zzam ya waiwaya, ko ba shi yake miƙowa hannun ba. Ya ga dai shi yake bawa hannu, ya miƙa masa hannu suka yi musabaha. Viper ya rungume shi, ya yi ajiyar zuciya ya ce "Na gode, ina sane da dukkanin gwagwarmaya da ka yi a kaina, duk dan saboda soyyayar da ka ke yi wa jauhar, da kuma ƙoƙarin ɗaukar fansa ta hanyata. Ka yi amfani da ni, ka cimma burinka, ba butulu ba ne ni, da na rintse idanuna daga kallon abin da ka ke yi mini, ina matuƙar kishin matata ne. A karo na babu adadi, ina mai sake baka haƙuri, ka yi haƙuri da Nabila kamar yadda jauhar ba ta kasance taka ba, Nabila ma haka, mussaman da ake barin halak dan kunya, a wannan karon ma ita ma ɗin tawa ce. Na gode sosai da gudunmuwar ka". Alhaji mu'azzam kawai ya yi murmushi ya ɗan daddaki bayan Viper ya ce "Ina tayaka murna, maganar Nabila kuma, ba a sanin ma ci tuwo, sai miya ta ƙare". Nabila kuwa hankalinta ne ya kai kan Naja'atu Bunkure da take yi wa 'yan jarida bayanin cewa, za su ɗaukaka ƙara. Ta gama bayanin ta nufi motarta, Nabila ta nufi in fa take, Sumayya ta riƙe ta, amma ta fizge ta nufi Bunkure. Ayshercool 08081012143 96 Tsayawa Bunkure ta yi cak, tana jiran Nabila ta ƙaraso, Nabila ta ƙarasa gabanta tana wani irin huci, kamar fusatacciyar damusa. 'yan jarida na ganin haka, abin nema ya samu, yuuuu suka ɗiba suka nufe su, da abin magana da camerori. "Ina fatan yanzu kin tabattar da jinin 'yar uwata ba zai taɓa tafiya a banza ba? Kuma matsayin da ki ke taƙama da shi, ki ka ce ba zan taɓa taka shi ba, ashe ba matsayin ba na arziki bane ba, na gode Allah da ki ka haska mini ko ke wacece, ban ci gaba da yi miki makauniyar soyyaya ba. Abin alfahari shi ne kayi amfani da damar da Allah ya baka, wurin kyautata wa mutane, yadda ko bayan ranka zaka yi alfahari da hakan, ba yin mugunyar shuka ba, da sharrinta zai ta bibiyarka har bayan ranka ba. Na ji ki na iƙirarin ɗaukaka ƙara, to baki da wannan lokacin, ga copyn ƙorafin da zan shigar a kanki nan, ga hukumar shari'a, kuma ina fatan ta soke lasisinki da na ƙungiyar ki, ta ƙwatowa al'umma hakkinsu da ki ke dannewa, ta hanyar rufe kura da fatar akuya, ki na kare yaran masu kuɗi, kina tozarta masu ƙaramin ƙarfi. Bakk da lokacin ɗaukaka ƙara, zai fi kyau ki mayar da hankali a kan yadda zaki karenki" Nabila ta dangwara mata wani file, tare da yi mata kallon banza. Tabbas tarihi ya maimaita kansa, domin kuwa sowa aka ɗauka da tafawa Nabila, yayin da ta bar Bunkure baki buɗe ta rasa abin cewa, ƙanƙanwar bayanta, da da auren wuri tayi, da ta kusa haifar Nabila, duk yadda ake girmamata kamar wata abar bauta, ita yau Nabila ta dizga kuma ta kayar a shari'a, wani malolon takaici ya ƙuleta, ta watsar da File ɗin, za ta shige cikin mota. Wani abokin aikinta ya ce "Kul, kar ki yar ki tafi da shi ki je ki duba, ki ga ta ina zaki ɓullowa lamarin". Nabila kuwa wurin Barrister Habib ta waiwaya, da ya kammala wata Shari'a ya fito, yana ta yashe mata baki, "Congratulations our legit barrister" Cikin murmushi mai haɗe da farinciki, ta ce "Na gode barrister, Allah ya saka da mafificin alkhairi. Har duniya ta naɗe ba zan manta da kai ba, a lokacin da yan uwa abokan aiki suke yi mini kallon mara hankali, na ɗaukko dala babu gammo, ka tsaya tare da ni, tare da bani ƙwarin gwiwa da gudunmawa ta kowacce fuska" Yayi murmushi ya ce "Honorable Mu'azzam Wada kankarofi shi ya dace ki yi wa wannan yabon, duk ƙoƙarin sa ne ya kawo haka" Ta dubi Alhaji mu'azzam ta ce "Honorable, ban san me zan ce maka ba, sai dai ina fatan idan kujerar sanata alkhairi ce a gareka, Allah ya baka, ina kyautata maka zato, halacci da taimakon da ka yi mana, Ubangiji Allah ya shaida ya kuma biyaka, bamu da baki, ko wani kalami da zamu yi amfani da shi, da zamu yi gamshashshiyar godiyar da za ta wadaci hidimar da ka yi mana, mun gode sosai da sosai" "Babu komai Nabila, yi wa kai ne, kun cancanci hakan ne, daga ke har Al'amin" Walid ya ce "Shikenan Alhamdilillah, zaman rami ya ƙare, mun yi 'yanci, kumurcin cikin rami zai yi yawonsa freely a gari, Allah ya sa kuma kar ya addabi al'umma da sara" murmushi Viper ya yi. "Yaya" suka ji an faɗa daga nesa, suna juyawa Shahida ce ta taho da gudu, ta ruƙunƙume Viper tana kuka. "Yaya dama zan sake ganinka? Yaushe rabon da na ganka a rayuwata, ashe zan sake haɗuwa da kai?" Wani irin sanyi ne ya ratsa Viper, duk da ba wani good time yake yi da Shahida ba, amma atleast yar uwassa ce ta jini, kuma duk da irin cin kashin da aka din ga yi masa a gidan su, sosai take nuna masa tausayi da jin ƙai" Rungumeta ya yi, sai dai ya rasa mai ze ce mata. Ta ɗago tana kuma ƙare masa kallo, ta ce "Na je prison ban san adadi ba, ba a bari na ganka, ina yawan yin kuka, idan na tuna halin da ka ke ciki, ɗazu na ga text ɗin Abbu, wai na taho kotu an wankeka daga zargin da ake yi maka, ni ban san yana ganinka kuna haɗuwa ba, na yi kewarka sosai yayana" Ya riƙe hannayenta ya ce "Kin yi saurin girma Shahida, ƙarama ce ke fa, lokacin da aka tsare ni" Zata yi magana ta haɗiyeta ta ƙarfin tsiya, sakamakon arba da ta yi da Nabila, cakumar rigar Viper ta yi, tana nuna masa Nabila. Ya ce "Menene?" "Ba ta mutu ba?" Ya ce "Eh, amma ta dawo ne ta halarci taron kotu, ta ga yadda za a hukunta waɗanda suka kasheta, yanzu zata koma" Nabila ta ce "Kaiiii" Kiɗimewa Shahida tayi cikin matsanancin tsoro, Walid ya ce "Viper kai fa ka iya wasan banza wasu lokutan, ba fa ta san ainihin abin da ya faru ba, sai ka saka ta suma ai" Baba ya ce "Na ga alama ai, Shahida wannan ba Jauhar ba ce ba, twins sister ɗin ta ce Nabila" tayi ƙuri da ido, tana kallon Nabila. Liti ya ce "Ke kin taɓa ganin wanda ya mutu ya dawo ne?" Ganin Nabila ta samu nutsuwa, 'yan jarida suka cigaba da addabarta a kan tayi magana, tambayar da ta fi ɗaukar hankalinta, har ta ji zata iya amsata ita ce "Wane irin farinciki ki ke ciki a yau, ganin kin yi nasara a wannan shari'ar?" Tayi murmushi ta ce "Alhamdilillah, nayi farinciki sosai da sosai, dan wannan ce nasara mafi girma da na samu, tun bayan zamana cikakkiyar lauya mai zaman kanta, kuma in sha Allah yanzu aka fara. Sai dai na sadaukar da wannan nasara tawa kacokan, ga babana maganin kukana, abin alafharina baya goya marayu ginshikin da na jingina da shi, ya zame mini tsananin da na taka na cimma wannan nasara. Mutumin da ya saita ni a kan wani buri da ban taɓa tunanin ina da shi ba, kuma zan ci karo da shi ba, yau gashi wannan burin ya cika wato Major Yusuf maitama mai ritaya, ina alfahari da kai dattijon arziki matuƙa gaya. Ina fatan al'umma za su ci gaba da bamu goyon baya ɗari bisa ɗari wurin kawo gagarumin gyara da sauyi, a fannin shari'a da kuma harkar tsaro. Kuma ina fatan matasanmu maza da mata zamu nisanci shaye-shaye da ta'amalli da miyagun ƙwayoyi". Yanayin yadda Nabila take magana, ya sanya Viper ya kalli Shahida ya ce "Jauhar zata iya magana haka doguwa a gaban mutane cike da ƙwarin gwiwa ba tare da tsoro ba?" Shahida ta girgiza kai ta ce "A'a" "To Nabila daban jauhar ma daban, wannan 'yar biyunta ce" "But how, ban taɓa sanin tana da sister ba ai" Viper ya ce "Is a long story" Abbu abin har mamaki ya bashi, yadda a wannan karon, Viper ya sake da Shahida, duk da a baya, duk da irin shishishigi da take yi masa, baya saurarar ta. Viper ya gabatarwa da Nabila Shahida, Nabila ta ce "Ai naga kamar haryanzu tsorona take ji, bari idan ta sake ta ƙara tabattar da ba jauhar ba ce, sai mu yi magana" Wata ƙatuwar helux ta shigo harabar kotun, baƙa ƙirin sai ƙyalli take yi. Ta yi parking a gaban su Nabila, da Abbu, wasu zaratan ƙarti ne suka saukko, su na sanye da riguna baƙaƙe da tambarin dragon, bayan rigar kuma hoton maciji ne da sunan Viper. Murmushi ne ya suɓucewa Viper, suka jeru suka din ga gaisawa sa shi ɗaya bayan ɗaya, suna yi masa congratulations da rungumarsa, yana amsawa cikin sakin fuska. Suka gaggaisa da su Abba, sai dai girmamawa ta musamman suka yi wa Alhaji mu'azzam. Viper ya ɓalle rigar jikinsa, rigarsa ta ciki irin ta su ce. Ɗaya daga cikin su, ya ce "Oga yana son ganinka, shi ya ce mu zo mu tafi da kai we need to celebrate with you" Ya jinjina kai ya ce "Ok to" ya kalli Baba ya ce "Baba bari na tafi, Nabila za a mayar da ita gida, idan na nutsu za ayi maganar in da yafi security ta koma, idan kuma za ta ci gaba da zama da madam shikenan. Shahida, zan zo gida zan yi miki gaisuwa ban in sha Allah. T ladan ina godiya sosai da sosai" ya ƙarasa maganar yana jinjina musu hannu, ya ce "Mai laya zamu yi magana, mu haɗe a chamber" yayi maganar yana danƙar kwalar ɗan mama ta ƙeya ya tura shi cikin motar" Liti ya ce "Wai yaushe zaku daina munafurtarmu daga kai har ɗan maman, waɗan nan jibga-jibgan kamar kai su kuma suwaye, menene alaƙarka da su?" "Tambaye su mana" Viper ya yi maganar yana nuna masa su. Ya kalli Nabila, yayi mata alama da hannunsa na zai kirata a waya, tare da kashe mata ido ɗaya. Murmushi ta yi ta ɗaga masa hannu, a daidai lokacin ya rufe motar suka ja, suka bar wurin. Nabila ta kalli Abbu jikinsa duk a sanyaye, Baba yana ta bashi haƙuri, ta ce "Baba da kai da honorable, yakamata ku shiga cikin lamarin nan  mussman kai, a sasanta Viper da Abbu, wallahi nayi nayi da shi yaƙi, da na fara maganar yake haɗe rai" Abbu ya ce "Na san kin yi iya ƙoƙarin ki Nabila, ki daina matsa masa, kin san murɗaɗɗen mutum ne, mai taurin kai, amma mai raguwar zuciya, duk wannan abin da yake yi, zai saukko, zan ci gaba da haƙuri, har zuwa lokacin da Allah zai sanya ya saukko". Viper ne a tsaye a wani katafaren office, wani narkeken mutum ya miƙe, ya ƙarasa wurin Viper, suka yi musabaha, ya rungume Viper ya ce "Congratulations my man" Viper ya ce "Thank you Sir" "Congratulations once again Al'amin" "Thank you very much sir" "Yarinyar nan fa ta bamu mamaki sosai da sosai, bamu taɓa zaton za ayi wining case ɗin ba, saboda case ne mai hatsari da sarƙaƙiya, amma thank God, Congratulations once again" Ya kalli ɗan mama ya ce "Anas" ɗan mama ya ɗan ɗago yana risunawa. "Yaushe zaka tafi training ne?" "Dan Allah sir ka yi haƙuri, ni ba sai na yi training ɗin nan ba, a bar ni kawai" Yayi murmushi ya ce "Viper ka ji abin da ya ce?". Viper ya ce "Bai isa ba sir, dole ya tafi" "To kai Anas, ko Viper bai faɗa ba, dolenka Anas, ai ka riga ka yi aiki da mu, you can leave, zan ganka" ɗan mama ya fice. Ya mayar da idonsa kan Viper ya ce "Viper, komai ya zo ƙarshe, yaushe zaka koma bakin aiki gaba ɗaya?" Viper ya ce "Ina son a ɗan ƙara mini lokaci, tun da ina gudanar da aikina daga nan, ina da abin da nake son ƙarasawa ne" Ya ƙaraso ya dafa kafaɗar Viper ya ce "Kamar haryanzu kana cikin pain Viper, amma yakamata ka tattara hankalinka wuri guda, a baka abin da za a baka ka cigaba da rayuwarka, amma duk abin da ka yanke shikenan, ina yi maka fatan alkhairi, zamu cigaba da baka dukkanin gudunmuwar da ka ke buƙata" Suka sake gaisawa da Viper ya fita. ***** Bayan Nabila ta koma gidan madam Halimaz tayu wanka ta canza kaya, madam sai murna take tayata saboda nasarar da suka samu, kai tsaye gidan Abba ta tafi, ta nufi benensa cikin matsanancin farinciki da murna, suna tare da Nasir, da wasu daga cikin yaran gidan da matansa. Gaban Abba taje ta zauna, tana ta murmushi bakinta yaƙi rufuwa, gaba ɗaya suka tattara hankalinsu a kanta. Dogon skirt ne a jikinta, da over size t-shirt ta Viper, tayi rolling da veil, ta ƙarasa gaban Abba ta durƙusa ta ce "Major Abba, na samu nasarar da ban yi zato ba, Alhamdilillah kotu ta wanke babban mai laifin da nake karewa, bayan da aka gano ba shi da laifin da ake zarginsa" Fuskar Major babu yabo babu fallasa ya ce "Na tayaki murna" "Abin da nake ta gaya maka kenan Abba, tun farko ba ka tsaya ka fahimce ni, nayi maka bayani ba" Ya girgiza kai ya ce "Nabila, ni fa duk wani abu da ya shafi mahaifinki ba ƙaunarsa nake yi ba. Da bai aura mata ɗan daba ba, da duk haka bata faru ba, ai yana da wasu yaran, meya hana su ya aura musu shi, sai ita, saboda ba ta da galihu, ni fa mutuwar yarinyar nan, ƙara mini ƙiyayyar mahaifinki ta yi, and na baki zaɓi idan zaki zauna a nan ne ki zauna, idan kuma wurin mahaifinki zaki koma, ki sauka lafiya ki yi abin da ki ke so, you are allowed to make decision" Jiki a sanyaye Nabila ta saki hannunsa, ta kalleshi ta ce "Abin har ya kai ga haka Abba? Ban taɓa tunanin akwai ranar da za ta so, ka sanya na ji wani abu a raina, mai kama da ba kai ne mahaifina ba" Ya dubeta a tsanake ya ce "Amma ke kin tabattar da duniya ba ni na haife ki ba" Ta girgiza kai ta ce "Ban nuna wa duniya ba kai ka haife ni ba, amma ina neman afuwarku baki ɗaya" ta tashi gwiwa a saɓule ta bar ɗakin. Ta sha kuka sosai da sosai a ɗakinta, sam ba ta ji daɗin abin da Abban ya yi mata ba. Ta koma ɗakinta ranta babu daɗi, tana jin kamar dan ba Nasir ne yayi nasarar ba, shiyasa Abban yake yi mata haka, ba wai dan yana jin haushin Babanta ba kawai" Baba Magajiya ce ta din ga rarrashinta, tana ba ta haƙuri, wayarta ce ta fara ringing, ta duba taga Viper ne. Ta ɗaga tare da goge hawayen da yake kwance a fuskarta. "Hello vi" "Ina waje" "Ai ba na barrack ina gida" Ya ce "Na sani, location ɗinki ya nuna mini, am tracking you ai" Ta ce "To ina zuwa" "Baba Magajiya, bari na je waje ana nemana" "To shi sirikin nawa ne?" Nabila ta ɓata fuska ta ce "Wane siriki kuma? Ai wallahi baba magajiya duk kallonku kawai nake yi, babu wanda ya yi mini kara a gidan nan, na zuwa in da mahaifina yake gaba ɗaya ma kamar kowa gaba yake yi da ni" Magajiya ta ce "Haba dai Arfa, wallahi dan babu yadda zan yi ne, amma ina matuƙar son yin hakan, amma kin ga ga a halin da ake ciki ne, kar nima na yi wani laifin" Nabila ta ce "Shikenan" ta tashi ta fita. "Vi snake" ta faɗa tana murmushi. "Kukan me ki ka yi kuma? Wai dan Allah ke a rayuwarki ba kya gajiya ne?" Ta girgiza kai ta ce "Ni kaina na san saurin kukan nan yana cutata, ba yadda zan yi ne" Ya ɗage kafaɗarsa ya ce "Ya gajiya kuma?" "Alhamdilillah, babu gajiya" "Bangajiya na dawo na yi miki, kuma na ƙara jaddada godiyata a gare ki" Ta numfasa ta ce "Kar ka damu, kaina na yi wa ai" "Gaskiya ne, gobe in Allah ya kaimu zamu koma wurin likita ko?" Ta jinjina kai ta ce "Eh gobe in Allah ya kaimu ne" Viper ya ce "Ina son 1hr kacal a lokacinki idan mun dawo" kawai ta gyaɗa masa kai. "Wai ya na ga jikinki a sanyaye ne, kamar ba wannan ranar ki ke jira ba? Meyafaru ko wani abin kuma nayi?" Ta girgiza masa kai alamar a'a. Ya sake kallon fuskarta yadda take ƙifta ido cikin damuwa. "Abla" ta ɗaga mayanyan idanunta ta na kallonsa. "Menene kuma?" "Abba ba zai yadda su sasanta da Baba ba, na rasa wace irin zuciya ce da shi, wai haushin sa ya ƙara ji, da ya aura maka jauhar, meyasa a cikin yaransa bai aura wa wata a yaransa ba, sai ita, saboda marainiya ce babu mai tsawatar masa. Shikenan haka zan zauna a tsakiya gaba ɗaya komai ya fita daga raina" ta yi maganar tana ƙoƙarin mayar da hawayen da ke shirin zubo mata. "Yanzu ni ne dai matsalar kenan?" Ta ce "A'a, ba kai ba ne ba, ya ma ƙi saurarata balle in yi masa bayani. Yanzu a haka zan ci gaba da zama a gidan nan, Abba ya kware mini baya a gaban mutanen gidan da ba sa so na, ko kuma can gidan mahaifina zan koma, na zauna a cikin waɗanda suka muzgunawa mahaifiyata da 'yar uwata. Zamana a cikin barrack na ɗan lokaci ne, kuma saboda kai ne, da komai ya kammala dole na bar zaman wurin, gaba ɗaya zuciyata a cunkushe take na rasa mai ma zan yi, na zata da an kammala shari'a komai zai zo da sauƙi, ashe tsugunno ba ta ƙare ba" Ya gyara tsayuwarsa ya ce "Ni ne matsalar a nan, zan kuma san abin yi na warwareta in sha Allah, ki yi haƙuri komai zai daidaita" Ta ce "Tayaya kenan, ka san halin Abba kuwa?" "Eh mana, hali mai kama da nawa ko? Zan san abin yi, ki je mu haɗu gobe in Allah ya kaimu" **** Nasir ya rasa abin da yake yi masa daɗi, mussaman yadda Nabila tayi nasara a kotu, duk sai ya sha jinin jikinsa, gashi sai ya ga kamar Abba ya sauya masa. Da asuba Abba yana sauraren labaran asuba, aka sako Muryar Nabila, tana murna da godiya ga Allah, bisa nasarar da suka yi a kotu, tare da sadaukar da nasarar ta ta gare shi baki ɗaya. Yayi shiru yana saurarenta, ƙasan zuciyarsa yana cike da farinciki, sai dai haushin mahaifinta, ya hana shi sakewa ya ji daɗin hakan. **** Ramma ta ɗauki wayar mama ba ta sani ba, ta kira Nabila, suka gaisa Ramma ta ce "Anty Nabila, mama ta ce wai kun yi nasara a kotu ko?" "Eh rahama, Alhamdilillah" Ta ce "Masha Allah, ina tayaku murna sosai da sosai Allah ya ƙara nasarori" "Amin rahama, mun gode sosai ya jikinki, lokacin zuwa awo bai yi ba ai ko?" Ta ce "Eh saura sati biyu" Nabila ta ce "To Allah ya raba lafiya" Sai kuma tayi shiru, ta kasa faɗar abin da ya sanya ta kiratan" "Rahama ko akwai wani abu ne" Jiki a sanyaye ta ce "A'a dama...." "Dama me? gaya mini babu wani abu" "Cewa na yi kin je wurin doctor ne? Ya warke?" Nabila ta yi murmushi ta ce "Allah sarki ƙanwata, na fahimce ki, ki yi haƙuri sai Allah ya kaimu lokacin awonki, daga nan sai mu je ki ganshi, kin san halin yayanki, daga ni har ke sai ya tijaramu ba ruwansa" Ta ce "To na gode sosai Anty Nabila" "Kar ki damu, ki cigaba da addu'a, da kula da kanki da cin abinci da shan magani, in sha Allah komai zai wuce" Ramma ta ce "Ina yi, na gode sosai" suka yi sallama. ***** "Viper, wai ɓoye-ɓoyen me ku ke yi mana ne kai da wancan munafukin yaron, ku na ƙulla wani abu da bamu sani ba, Menene alaƙarka da sojoji. Gashi kullum cikin danna wanan wayar ka ke, wadda ba a gane komai sai lambobi da locations, me ka ke yi?" Liti yayi maganar yana tsare Viper da ido. "Shaƙeni sai na gaya maka" Walid ya ce "Ba maganar shaƙewa ba ce ba, maganar gaskiya ce, ka gaya mana me ka ke yi wanda ba mu sani ba?" "Sirri ne, ba a faɗa" Liti ya ce "Ƙarshen sirri dai ace ƙungiyar asiri ka shiga ko? To komai sirrinsa gaya mana, mu yanzu har akwai wani sirri da za a ɓoye mana?" Kallonsu ya din ga yi ɗaya bayan ɗaya ya jinjina kai, ya ce "Idan kun matsa na gaya muku, zan gaya muku amma wallahi a yanzu,na gaya muku sai kuma kun yi irin abin da nake yi, komai wahalarsa da azabarsa" Walid ya ce "Azaba wacce ce ba mu gani ba, mu na jinka" Liti ya ce "A'a tsaya gaskiya, ya ce wallahi fa, ina dalili ban san wace kalar azaba ce da wahala ba, ni dai na haƙura riƙe kayanka, ba na son ji ɗan mama ya gaya mini, dan na ga tare ku ke ƙulle-ƙullen" "Shi ma ba zai gaya maka, saboda yana cikin tsaka mai wuya yanzu, sanin abin da nake yi ya tilasta masa yin irin aikina, ina ga ma ba zaka sake ganinsa ba, yana can a tsare, cikin satin nan zai bar gari" "A kai shi ina kuma?" "Liti yayi maganar yana kallon Viper" Viper ya yi murmushi ya ce "Irin ƙaunar da aka nuna mini, ta azaba, ita zan yi masa domin inganta rayuwarsa, abin da zan yi masa kenan na tabattar masa da na ji daɗin halaccin da ya yi mini" "Ta hanyar gana wa mutum azaba? Ni dai ba da ni ba dan Allah, ka riƙe halaccinka" Walid ya ce "Ina jinka, gaya mini koma menene" "Ya fa rantse mai laya, ka san halin Viper, tun da ya rantse abin babu sauƙi, ni dai a bari na fita sai a faɗa" Walid ya ce "Munafuki so yake fa ya ji koma menene ɗin" Viper yayi murmushi ya ce "Ni dai na rantse, shawara ta rage taku" Liti ya ce ba ya son ji, Walid kuma ya dage sai ya ji. Ƙarshe dai ya ci gaba da yi musu yawo da hankali ya ƙi gaya musu. *** Kamar yadda suka shirya, washegari suka tafi Asibiti ganin likita, suna tafe a hanya take gaya masa ramma tana yi masa murnar samun nasara da ya yi a kotu. Kawai ya ce "Hmm" "Hmm kuma kamar yaya?" "Kawai ina tuna wautar da yarinyar nan tayi ne" Nabila ta yi murmushi ta ce "Kar ka zargeta Vi, so ne sila, amma yanzu idan ya fito yaya za ku yi da su ne, dan ko da me ku ke yawo ba zai saki rahama ba, ban taɓa tunanin ana irin wannan son a gaske ba gaskiya" Ya ce "Abin da mahaifiyarta ta yanke kawai, ni dama babban fatana a hukunta shi, maganar aurensu ni bani da abin cewa" Nabila ta ce "Vi dan Allah ku yi haƙuri, ku yafe wa gayen nan, yayi nadama kuma wallahi suna son junansu da rahama, ku bar masa kayyasa, tasa ce" "Ba za a bashin ba, bashi da nasaba mai kyau" "Vi sai ya ci albarkacin ku, nasabar tasa ta gyaru, wallahi ni gaba ɗaya karya mini zuciya ya yi, dan Allah a bar masa ita, yana sonta sosai" "Anƙi" "Vi baka san menene so ba, ba ka san zafinsa da wahalarsa ba" Ya ce "Eh ban sani ba, kuma bana fatan na sani. Ke da liti ban san wanda ya fi wani raina ni ba, shi ya ce ba zan sake yin aure ba, na shiga ittikafi, ke kin ce ban san so ba, ina ga ni duniyata daban, ba a jinsin mutane nake ba" Sosai Nabila take dariya ta ce "To mutum ne kamar boss, kullum rai a haɗe kullum cikin tsare gida, dole a yi tunanin baka jin komai, da ya shafi soyayya" Tunawa yayi da Jauhar ta taɓa gaya masa magana makamanciyar wannan. "Ba na tunanin akwai wanda so ya azabtar kamar ni, a lokacin ban san menene shi ba. Ranar da na fara ganin jauhar, ta ganni rungume da liti cikin jini, ta ƙwala ihu ta suma. Haka kurum gabana yayi mummunar faɗuwa, na je na ɗagata na ga ta suma, tun daga ranar nake yawan mafarkinta, da na tuna a yanayin da ta ganni, za ta yi zaton kisan kai nayi, sai na ji babu daɗi na damu, har zuwa lokacin da Allah ya haɗamu a inuwa ɗaya, tsarki ya tabatta ga Ubangiji mai jujjuya al'amura yadda ya so, a lokacin da ɗan Adam bai taɓa tsammanin faruwar abin ba. Allah ya jiƙan Zahra" Jiki a sanyaye Nabila ta amsa da Amin, tare da jin begen ina ma ko sau ɗaya ta ga jauhar a rayuwarta, tana matuƙar jin daɗin yadda ake faɗar kyawawan halayenta. Viper ya ga likita kamar wancan lokacin, ya bashi shawarwari, sai dai a tattauanawar da suke yi ne, likita zai gano bakin zaren, sai dai fafur Viper ba ya son magana, sai dai Nabila ta yi ta ɓaɓatun itakaɗai. Bayan sun fito sai da suka je gidan su Ramma, suka gaisa, Viper da maman suka din ga hira, Nabila kuma suka shiga ɗaki da ramma. Sai azahar suka bar gidan su ramma, Nabila ta yi ta rarrashin ramma, ta kwantar mata da hankali. Bayan sun fito wani store ya kai Nabila, ya ce ta ɗauki duk abin da take so. Ta kalleshi ta ce "Meyasa ka kawo ni nan, ina fatan ba biyana kuɗin aikin da na yi zaka yi ba, ka riga ka biyani, haɗa ni da mahaifina bana buƙatar komai daga gareka, komai na yi maka kaina na yi wa" "Ai bani da abin biyanki, dake da iyayenki, bani da abin biyanku, wani ihsani ne kawai, wani abu da na daɗe ina burin in ga ina yi wa jauhar, a lokacin ba ni da halin hakan, amma tun da gaki sai na yi miki a madadinta" Tayi murmushi ta ce "Na gode sosai da sosai Vi, amma idan ka yi mini haka, zan ga kamar ka biyani ne abin da na yi maka, maganar gaskiya ba zan iya yadda ka yi mini sayayya ba, domin hakan tamkar cin amanar jauhar ne, kuma kaga Jauhar daban ni Nabila ma daban". Ayshercool 08081012143 97 Shiru yayi yana dubanta, domin ya tabattar idan da gaske take, sai dai yanayin fuskarta ya tabattar masa da gaske take yi ba wasa ba. Basarwa yayi ya ce Shikenan su tafi, amma deep down ya ji zafin abin da ta yi masa nesa ba kusa ba, he wish 'yar madararsa tana raye, da ya san ita ba zata watsa masa ƙasa a ido ba, kamar yadda Nabila ta yi yanzu ba. Dan rashin kunya, su na tafiya a hanya kuma, ta na yi masa hira da surutu, ganin ya yi mata banza, ya sanya ta ja bakinta ta tsuke, kuma ta tabattar fushi ya yi. A hanya ya sauka, ya bar ta da Joseph, ya mayar da ita gida, shi kuma yayi nasa wuri. **** Washegari da yamma, Abba yana gidan gonarsa, yana office ɗin sa, ana ta fitar da ƙwai na kaji, da na sauran tsuntsaye ƙaton gidan gona ne sosai da sosai, gidan gonarsa na cikin manyan gidajen gona da yake fitar da ƙwai, har maƙwabtan garuruwa. Da su kansu kajin da kifaye, ban da sauran dabbobi. Masinja ya sanar da shi ya yi baƙo, Abba ya ce a shigo da shi. Mintuna kaɗan aka buɗe ƙofar Office ɗin aka shigo, ajiye biron hannunsa ya yi yana kallon Viper. Viper ya yi sallama, Abba ya amsa a hankali yana ci gaba da kallonsa. Ya ƙaraso ya tsaya, ya gaida major cikin girmamawa kamar yadda suke yi a tsakaninsu masu ɗamara, hakan ya tabattar wa Major akwai wani abu tattare da baƙon nasa. Ya bashi dama ya zauna. Viper ya ce "Duk mun taɓa haɗuwa ba na da tabbacin ko ka gane ni, amma bari na sake gabatar maka da kaina, sunana Al'amin Ibrahim, wanda 'yar ka Nabila ta tsayawa a kotu, kuma mijin 'yar uwar Nabila da Allah ya yi wa rasuwa" "Mijin wadda ka kashe dai, da babanta bai san ciwonta ba ya ɗauketa ya aura maka. Ta yaya zan kasa ganeka, da ka ɓata mini shirina na shekara da shekaru ka ɗauki Nabila ka haɗata da babanta, mutumin da bai martaba rayuwar uwarta da ta 'yar uwatta ba har ya iya aura maka ita ka kasheta". "Ba ni na kasheta ba, kamar yadda kotu ta tabattar kuma ta wanke ni, ina roƙonka saboda Allah, kar laifin da ba namu ba ya shafe ni da ni Nabila, mussman ma ita. Makamancin abin da ya faru da Jauhar, irinsa ne a rayuwata, da ya jefa ni cikin ƙaddara. Duk wannan mummunar rayuwa da nayi, ta samo asali ne daga rashin samun ingantaccen bangon da zan jingina rayuwaya da shi, sai da ƙaddara ta saka aurena da Jauhar, ba zan taɓa mantawa da ita ba har duniya ta naɗe, kuma ban kashe jauhar ba. Kamar yadda kotu ta tabattar, duk da na fuskanci mutum ne kai irina, muna amfani da ƙwaƙwƙwarar shaida da muka gani a zahiri ne, ba dan haka ba, ba zan so na baka wata gamshashshiyar hujja da shaida da zata tabattar maka da Nabila a kan dai-dai take, kamun da aka saka ɗanka yayi mini ba bisa ƙa'ida bane ba. Da fari hukumar'yan sanda ce ta bashi umarnin, daga baya kuma an bashi maƙudan kuɗi dan ya kama ni, hakan ya sanya ya din ga ɓata Nabila a idonka. Duk ban gaya maka wannan abun da raba maka kan iyalinka ba, roƙonka kawai nake yi, ka daina fushi da Nabila, duk da ganin mahaifinta da ta yi, a duniya ba ta da wani wanda ta shaƙu da shi take ƙauna sama da kai. A madadinta ina mai ƙara baka haƙuri, domin kuwa na san duk ni ne silar komai, amma dan Allah na roƙe ka, ka yi haƙuri ka yafe wa Nabila da mahaifinta, ci gaba da fushi da ita, zai kua jefa rayuwarta a cikin damuwa" "Ka gama?" Major ya yi maganar yana kallon Viper. Viper ya yi shiru bai ce komai ba. "Na ji na kuma gode, amma ka tashi ka tafi, ka ɓata ruwa ba domin ka sha ba, ka ɓata mini haɗin kan iyali" "Abba ban ɓata maka kan iyali ba, son abin duniya ne ya rinjayi Nasir, ya ƙara ta'azarra al'amarin, ina sake baka haƙuri, saboda Nabila kar azo ta shiga wani halin" ya na gama maganar ya tashi tsaye ya fice daga ofishin. Bayan fitarsa Major ya yi shiru yana kallon ƙofar da ya fita, da nazartar maganganun da ya yi. Gaba ɗaya Viper ya daina kiran Nabila a waya, ita ma kuma ba ta neme shi ba, hakan ya ƙara tunzura shi, ganin yadda ta watsar da shi gaba ɗaya. Major ya so ya yi wa Nabila maganar zuwan Viper in da yake, amma yayi mata shiru ya rabu da ita. ***** Satin awon Ramma ya zagayo, Nabila ta je ta ɗauki ramma, suka je asibiti. Aka yi mata awo aka duddubata, komai nata lafiya ƙalau. Su ka tsaya suka yi sayayya, suka tafi prison. Ramma sai murna take yi tana jin daɗi za ta ga Abdul. Saboda yadda Nabila ta zama popular yanzu, duk in da ta shiga an santa, tana samun alfarma, yau ma har ciki aka shiga da su. Aka je aka fito musu da Abdul, yana ganin ramma ya saki murmushi, ita ma murmushin ta sakar masa, ta miƙe tsaye ba tare da ta san ta miƙe ba. Nabila ta ce "Bari na baku wuri, idan kun gama ma gaisa" ta fita waje, bai damu da gandiroban da yake wurin ba, ya rungume abar sa. Ta ce "Doctor ya jikin ka warware?" "Inyee an daina gantsara mini sunana,  Abdul yasar" Ta saki murmushi ta ce "Ko dan saboda wannan ai yakamata na fara saye sunan" tayi maganar tana nuna masa cikinta, da ya kai watanni shida ya fito sosai. Murmushi yayi ya zira hannunsa cikin hijjabinta, ya shafa cikin nata. "Ina fatan dai wurin awon babu wata matsala da babyn namu?" Ta ce "Anty Nabila tana kula da ni sosai, tana kai ni awo" "To ki na cin abincin da shan maganin dai ko?" Ta jinjina kai ta ce "Eh, kawai dai ina son na ga ka fito ne, ina cikin damuwa tsareka a wurin nan" Ya kalli wurin ya ce "Kar ki damu, ai na riga ma saba kuma ba wata wahala nake sha ba your excellency, kewarki nake tayi ne dai kawai, amma yaya zasu bar mu mu cigaba da zaman aurenmu?" Ta rausayar da kai, ta ce "To gashi nan dai, ban san ya ake ciki ba, basu sake cewa komai ba. Ina son in roƙi Anty Nabila, ta ɗan ƙara lallaɓa mini su, amma nauyinta nake ji". Ya ja hannunta suka zauna, ya ce "Ni zan roƙeta, ko sake durƙusawa zan yi a gabansu na basu haƙuri, ni dai su bar mini ke babyna, da ke jaririnmu mu rayu tare ko Rahamana?" Ta jinjina masa kai, ta numfasa ta ce "To yaya yanayin abincin kana samu ka ci kuwa?" "Eh mana, komai nawa normal kawai dai ina tsare ne, ki kwantar da hankalinki, ki rainar mana babynmu, ina fatan lokacin da zan fito yayi dai-dai da lokacin da zaki haihu, a karɓi haihuwar nan da ni. Na so ni zan kula da ke ayi rainon cikin nan da ni" "To yaya zamu yi, kana naka Allah ya sa shi ne dai-dai, Allah ya fito mini da kai lafiya" Abdul ya dafa kafaɗarta ya ce "Naki ne ni?" Ta jinjina masa kai cikin jin kunya tana murmushi. "Naki ne ni rahama, ƙaddararmu ce ta zo mana a hagunce, amma mun gode masa Allah ya sassauta mana, ya sanya su barmu mu yi rayuwarmu ta aure" Ta ce "Amin, bari ta zo ku gaisa, mu tafi, na san yanzu za su ce mu tafi" Ya marairaice ya ce "Haba dai, kwata-kwata yaushe ku ka zo, ban gaji da ganinki ba, yayi maganar yana sumbatar goshinta. Gandiroba ya ce "To sharokhan baban soyayya, lokaci yayi" Abdul ya yi murmushi ya ce "Ai shi sharokhan na shi film ne, ni kuwa soyayya ce ta zahiri, dan haka ni na fi shi ma" yayi maganar yana dariya. Nabila ce ta dawo, suka gaisa da Abdul, sai dai da ta ga farinciki a fuskokinsu, sai ta ji daɗi. "Ina godiya sosai da sosai, rahama ta gaya mini yadda ki ke kula mini da ita da babyna, Allah ya saka miki da alkhairi" Nabila ta ce "Amin, ai yi wa kai ne, rahama ƙanwata ce, ina jin daɗin ganinta cikin farinciki. Nayi mamakin yadda aka yi ka yi mata laifi kamar wannan kuma ka iya dasa soyayyarka a cikin zuciyarta. Meye sirrin ne?" Yayi murmushi ya ce "Ita zaki tambaya ai" Ramma ta harare shi ta ce "Ba wani sirri, ban da faɗa me ka iya?" "Soyayya" ya bayar da amasa kai tsaye, da sai da ramma ta ji kamar ta nutse. Suka yi dariya, ya sake cewa Nabila "Dan Allah na ga kamar ke kina tausaya mana, dan Allah ki rarrashi mama, ki ba ta haƙuri su bar mana aurenmu dan Allah" Nabila ta sauke numfashi ta ce "To bani da ta cewa ne, idan na matsa yayanta hayayyaƙo mini zai yi, amma zan lallaɓa ta ɓangaren mama na cigaba da shawo kanta, in sha Allah komai zai wuce" Ya ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya saka da alkhairi. Idan da wani abu ko kuɗi sun yi kaɗan, ayi mini magana" Nabila ta ce "Kai wane irin kuɗi sun ƙare, wannan maƙudan kuɗi har haka, akwai kuɗi sosai in sha Allah ba wani abu" Ya ce "To shikenan, muna godiya sosai barrister, babyna sai yaushe kuma?" Ramma ta galla masa harara, amma bai fasa ba, ya riƙe hijjabinta, ta waiwayo ta fizge ta na murguɗa masa baki. Shafar sumar kansa ya yi, yana dariya, suka fice ita da Nabila. Suna tafe a hanya, Nabila ta ce "Ramma har mamaki ku ke bani da ke da Abdul, dan Allah me Abdul ya yi miki, har ki ka fara sonsa, duk da girman laifin da ya aikata miki?" Ramma ta jinjina kai ta ce "Na san da yawa ba za su fahimce ni ba, za a zata ko kwaɗayin wani abu ne na hannunsa, ko kuma wani abu nake yi wa, wanda ni har muka rabu ban san menene auren ba, kawai dai ina jin daɗin shiryuwar sa a dalilina. Kuma yana da wasu nagarta, wanda shi kansa bai san yana da ita ba. Da ya samu isashshiyar tarbiyya, ba zai yi wasu abubuwan ba. Ya nuna tsantsar nadamarsa, gani nake idan na rabu da shi, zai iya koma wa ruwa, duk da da gaske, yake tuba a kan abubuwan da yake aikatawa. A matsayin ya aureni, ya tabattar mini da ya aure ni, babu irin zagi da rashin mutuncin da ban yi masa ba, amma ko a jikinsa, bai taɓa damunsa ba, kawai zai yi abin da ya ga dace yayi domin ya kyautata mini, ko na yaba ko na kushe bai dame shi ba. Sannan daga halayensa masu kyau, yana da tausayi da taimako, mutum ne mai kyauta ta ban mamaki, kuma ya san aikinsa sosai da sosai, ina duba wannan abubuwan ne, amma ni kaina na san ta wani ɓangare kamar ban kyauta wa kaina da mama ba" Nabila ta ce "Kar ki ce haka, wannan shi muke kira da jarrabawa, Allah ya jarabce ka ya ga yaya zaka yi? Bar ganin Abdul ba ya ji, wallahi sai ki ga saboda yawan kyautarsa da taimakonsa, ya sanya Allah ya din ga ji da shi, maybe shiyasa ya sanya tsautsayin nan a tsakaninku, domin ya rabauta ya tuba, yadda ya daina zina within shot period of time da ku ka zauna, ya cancanci a yaba masa daga ke har shi, ina fatan Allah ya tabattar da alkhairi a zamanku, ya sanya sanadin shiriyar sa kenan, idan Allah ya tabattar da zamanku, ki yi ƙoƙari ki rufa masa asiri, ki zauna da shi da zuciya ɗaya, ki yafe masa". Ramma ta ce "In sha Allah Anty, na gode sosai da sosai, Allah ya nuna mana aurenku ke ma, da Yaya Al'amin" Nabila ta kalleta ta ce "Da wa? Wannan yayan naki ai sai Jauhar ɗin, Allah ya bashi mace ta gari dai ba Nabila ba" Cikin mamaki Ramma ta ce "Amma Anty Nabila saboda me? Wallahi yana da kirki, yana da faɗa ne dai kawai" "Wasu dalilai rahama, ki manta kawai, ba soyayya muke yi ba dama, kawai dai nima yayananne" Jiki a sanyaye ta ce "A'a shi sonki yake yi" "Yaya aka yi ki ka sani, shi ya gaya miki?" "Ni a wa zai gaya mini, bai gaya mini ba, amma wasu lokutan irin kallon da Abdul yake yi mini, yake yi miki. Idan mutane sun kai goma a wuri, duk wanda zai yi magana ba zai damu ba, amma da kin fara magana, zai tattara nutsuwar sa da hankalinsa a kanki. Ko wani abin ki ke yi daban, yana kallonki ta ƙasan idonsa" Kwashewa da dariya Nabila ta yi, ta ce "Kai rahama, haka ki ke saka masa ido kina kallonsa, ke duk a ina ki ka san hakan shi ne so?" "Wurin doctor, amma Wallahi yana sonki" "Daina rantsewa rahama, Viper mace ɗaya tak yake so a duniya, kuma yanzu ba ta raye, babu kuma macen da za ta iya maye gurbinta, dan haka ki manta kawai" Rahama ta ce "Shikenan, tun da kin ce haka, amma ai kamarku ɗaya ita, kema yana sonki, ina ga dai ke ca ba kya sonsa kawai" Rahama tayi maganar cikin sanyin jiki sosai, dan tana son ta ga sun yi aure, dan sun dace sosai. **** Abubuwa suka din ga damun Major, game da maganganun da Viper ya gaya masa, sai ya kasa haƙuri, ya kira Nasir ɗakinsa. Ya dube shi sosai sannan ya ce "Nasir tambayarka zan yi, kuma ina so ka ji tsoron Allah, ka gaya mini gaskiya" Ya ce "To Abba in sha Allah" "Waye ya saka neman yaron nan da Nabila ta kare?" Ya numfasa ya ce "Abba maitaimakin CP ne" Abba ya ce "Da kuma wa?" "Shikaɗai ne Abba" "Gaskiya na ce ka gaya mini, waye ya baka kuɗi a matsayin cin hanci, ya ce lallai ka nemo shi? Kar ka yi mini ƙarya, ka san nima tsohon ma'aikaci ne" "Ba kuɗi aka bani ba, senator ma'aruf Indabo ne" "A kan me zai saka ka nemo masa wani ɗan daba, menene alaƙarsa da ɗan daba yana sanata?" Nasir ya girgiza kai ya ce "Nima ban sani ba Abba" "Baka sani ba, kawai ka karɓa ka fara yi, Nasir idan baka ji tsoron Allah a kan aikinka ba, a tsiyace zaka shekara talatin kana wahala, ka gama aiki ka zama abin tausayi. Na fara yadda wasu abubuwan kai ka ta'azzara su, kamar Nabila ta fika gaskiya". "Abba mutumin fa ɗan daba ne, da yake zubar da jini, da aikata miyagun laifuka" Major ya ce "To meyasa ba ku nemi kama shi a kan laifin da yake aikatawa ba, wani zai ja ka gefe ya kuma tunzuraka, ba tare da ka san abin da ya haɗa su ba, Nasir ka san aikinka kuwa? Kaga tashi ka je kawai jeka" Ya buɗe baki zai yi magana major ya ce "Jeka ba zan sake magana da kai a yanzu ba, ina dai tunatar da kai muddin ka gauraya halal ɗinka da haram, babu in da zaka je wallahi. Kuma ka ji tsoron Allah, kar masu ƙarfi su din ga amfani da kai, a kan marasa ƙarfi, saboda kana saka wannan kakin lokaci ne" Sosai kunya ta kama Nasir, saboda yadda asirinsa yake nema ya tonu, na ya karɓi cin hanci, ya din ga matsawa Nabila da ƙoƙarin daƙileta a kan nata aikin. *** Cikin dare hasken farin wata ya gauraye ko ina, Viper na tsaye a bakin window, yana shan sigari, hannunsa ɗaya yana kallon wayarsa, kwanaki shida kenan rabon da su yi waya ko ya sanyata a idonsa, babban mamakin da ta bashi, yadda ƙiri-ƙiri ya nuna mata yayi fushi, amma ko ta sake neman sa. Haka kurum ya ji ya ƙara fusata. Ya harɗe ƙafarsa, yana ci gaba da shan sigarin, kawai sai watarana ta faɗo masa, Jauhar ta tsare shi a gida, ta hana shi fita ko ina, kuma ta bashi kara uku na sigari kawai. Cikin dare ta yi bacci, ya tashi ya fita tsakar gida, ya shiga banɗakin tsakar gida, ya sha son ransa, ya daɗe hayaƙin ya ragu, sannan ya koma ɗakin ya kwanta. Ashe tun da ya tashi ya fita, tana kallonsa, yana kwanciya ta tashi ta matso kusa da shi, ta saka hannu ta matsa bakinsa, ta sinsuna, dan ta tabbatar masa ta san me yayi, ba ta ce masa komai ba, ta juya ta kwanta. Kamar wanda ta kama yana alfasha, yayi tsuru-tsuru, ya rasa me ma zai ce mata, kawai ya basar. Aka jima yana ƙoƙarin ya rungumeta, dan ya mantar da laifin da yayi, ta tashi ta bar masa gadon, ta yi alwala ta tayar da salla. Asubar fari ba ta tashe shi ba, yaje masallaci ya dawo, a gida yayi azkar, ya din ga 'yan kame-kame, amma taƙi kula shi, har gari ya waye, sai da ya gaji ya ce "Ni fa guda uku na sha kawai ba da yawa ba" Ta kalleshi ta ce "Me fa?" "Sigarin" ta ɓata fuska ta ce "Hakan ya tabattar mini da zaka iya cin amanata wataran, ka yi abu ban sani ba" Ya girgiza kai ya ce "Ai uku ce kawai ba wata mai yawa ba, ki ke wani haɗe rai " "To Allah ya baka haƙuri, na ga kamar na matsa maka" daga haka ta ci gaba da sabgarta. Ranar ba ta hana shi fita ba, ya zauna bai fita ba, ko zata huce, har da yi mata aikin gida, amma ya kasa cewa ta yi haƙuri, ta tabbatar da ya sha jinin jikinsa, duk ya damu, amma ya kasa ba ta haƙuri. Duk sallolin ranar a jam'i ya yi su. Kafin ya dawo daga sallar isha'i, ta sha kwalliya, yana dawowa ta rungunmi abin ta, kamar ba fushi tayi da shi ba, iya punishment ɗin nan da tayi masa, sai da ya ji kamar ya shekara a prison. Jauhar akwai iya dealing ta cikin ruwan sanyi, a lokacin babu wani abin da yake shakka irin yi mata laifi, saboda ta riga ta sanshi, ciki da bai ta san hanyoyin hukunta shi. Sakin guntuwar sigarin yayi, ya koma ɗaki ya kwanta ya cigaba da tunaninta. Da haka wani nannauyan bacci ya ɗauke shi, sai dai kasancewar da ita ya kwanta a ransa, sai ya din ga mafarki da ita, mafarki mai cike da shauƙi da nishaɗi irin na ma'aurata. "Master salla fa, zaka rasa sallar asuba." tayi maganar tana shafa sumar kansa. Ƙanƙameta ya ƙara yi, yana tura kansa cikin wuyanta, da yake fitar da daddaɗan ƙamshin turaren da yake matuƙar son jin tashinsa daga jikinta. "Viper wai ina zaka shiga a cikin pillown nan ne? Wai ko dai ka sha wani abu bamu lura ba, tun ɗazu fa muke tashinka, ka tashi mu yi salla dan Allah" A hankali ya motsa, ya buɗe idonsa ya ga hasken fitilar solar, ya haske ɗakin, sai a lokacin ya lura da ya ƙanƙame pillow. Yayi miƙa tare da yin salati, ya kalli liti da yake tsaye a kan sa ya ce "Akwai gas ne?" "A'a ɗan kaɗan ne sosai, sai an yi refiiling ma zamu iya dafa karin kumallo". "Ɗora mini ruwa, ku yi sallarku zan yi wanka" "Wai Viper meyake faruwa ne kwana biyun nan, ko ka fara dawowa bil adama ne? Ni ina cewa ka yi wa addini hidima meyake faruwa" Ashar Viper ya yi masa, ba shiri liti ya ce "Allah ya baka haƙuri, ya ƙara lafiya" Walid kuwa dariya yayi, ya ce "Allah ya ƙara, uban son jin ƙwaƙwaf". Bayan sun karya Baba ya kira Viper a waya, ya ɗaga suka gaisa, ya ce "Aminullahi, dan Allah idan baka komai zuwa azahar ina son ganinka" "To Baba in sha Allah zan zo, nan gidan zan zo na same ka?" "Eh dan Allah" "Zan zo in sha Allah" "Yauwwa Allah ya yi maka albarka" Viper ya amsa da Amin. Ɓangaren Nabila ita ma kwanaki bakwan nan da suka yi, ba sa magana da Viper, abin ya dameta, ƙishirwar son ganinsa ta addabeta, ga ayyuka sun fara yi mata yawa, 'yat shaharar da tayi ta kwanan nan, ya sanya take ta samun cases ko ta ina. Ban da masu nuna suna sonta, manyan mutane da suke sonta da aure. Yau da mafarkin da tayi ta tashi a zuciyarta, mafarki tayi da mai kama da ita, wadda take da tabbacin jauhar ce. Tana nuna mata inuwar mutumin da yake ɗaure cikin sarƙa a baya, yanzu babu sarƙar, sai dai daga yanayin inuwar tasa, kamar a galabaice yake, duk da babu sarƙar sai tangaɗi yake yi. Tana murmushi ta cigaba da nuna mata shi, ta nufi in da take nuna mata, sai dai da ta waiwaya ba ta ganta ba, tana ƙoƙarin ƙarasawa in da mutumin yake, kawai ta farka daga baccin. A hankali ta furta Viper, a gurguje ta shirya, tayi ta trying lambarsa, amma yaƙi ɗagawa, ta din ga jin ko me zai yi mata, yakamata ta kira shi, ta ji ya yake. **** Ko da Viper ya je gidan su Jauhar, ya tarar da motoci a ƙofar gidan, bai damu da ko me ake yi ba, ya kira Baba ya ce masa gashi nan yana ƙofar gida. Baba ya ce ya shiga kawai, ya ƙarasa ya shiga, babu wanda ya kula a mutanen gidan, sai hafsa da suka gaisa ya shiga ɗakin Baba. Alhaji mu'azzam ya tarar, da Abbu, da kuma shi kansa Baban. Gefe ya samu ya zauna a ƙasa ya gaishe su, sai dai da ya zo kan Abbu kamar an yi masa dole, haka ya gaishe shi. "Ya gida ya ƙoƙarin Kuma?" Baba ya tambayi Viper. "Lafiya ƙalau Alhamdilillah" "Ina yan uwan naka?" Viper ya ce "Su na gida, nikaɗai na zo". Baba ya ce "babu laifi, Al'amin" "Na'am Baba" "Na san zaka yi mamakin kiranka da muka yi, babu tsammani da wuri haka. To bakomai bane ya janyo, Nabila ta same ni, tayi mini wata magana ne, kuma nima naga hakan yakamata, duba da yadda abubuwa suka wakana. Al'amin su iyaye, ba a fushi da su, kuma duk lalacewarsu iyaye ne, balle babu lalacewa a cikin iyaye, yakamata ka sasanta da mahaifinka, yanzu ina jauhar, ina mahaifiyarka, ina ɗan uwanka, ko da kuɗi ba zaka sake ganinsu a gidan duniya ba. Dan haka ka yi haƙuri, mun san mu masu laifi ne a wurinku, amma ku yi haƙuri a yafe ya wuce dan Allah ba dan halinmu ba". Viper ya yi shiru, kamar mai nazari amma bai ce komai ba. Abbu ya ce "Al'amin, nauyinka da nake ji, ya sanya na kasa nemanka gaba da gaba na nemi afuwarka, na san in dai dan halina ne, da abin da na aikata maka, ba zaka sake kallona a matsayin mahaifi ba, amma ba dan halina ba domin Allah. A ƙaddarar rayuwarmu, na ɗauki darasi da dama, daga illar da mutum zai yi wa rayuwarsa, shi ne auren mace domin buƙatarsa kawai, ba tare da tunanin abin da gobe ka iya haifarwa ba. Duk da ni a zatona dan gobenku na auri Rahila, amma ta ci amanata, kuma nima na san da laifina na rashin bibiya da tantance abin da take ɗora ni a kai, amma dan Allah ka yi haƙuri Al'amin, ka yafe mini ka dawo gida mu yi rayuwa a ɗan abin da yayi mini saura na rayuwata" Alhaji mu'azzam ya ce "Viper, ka yi haƙuri dan Allah, duk wani abu da ya faru, ya wuce tun da bawan Allah nan shi yayi silar zuwanka duniya, kuma wani abin idan bai yi maka ba, wani yayi maka, yana cikin tashin hankali da damuwa sosai" Viper ya numfasa ya ce "Ko a baya ni ban ƙi Abbu ba, ina matuƙar ƙawazucinsa da son kasancewa tare da shi, Abbu shi ne ya ƙi ni ya kore ni, amma tun da yanzu ya nemi na dawo shikenan, ya riga ya wuce. Amma ni a yanzu na girmi zaman gida, ba zan iya rabuwa da su Walid ba, sai na tabattar da rayuwarsu ta inganta suma, kamar yadda suka rayu da ni lokacin da kowa yake mini kallon mara amfani. Kuma idan na koma gidan nan, zai iya cigaba da haddasa husuma, wanda ni kuma bana fatan hakan". Abbu ya ce "Hakan ma na gode Al'amin, Allah ya ƙara shirya mini kai, dan Allah idan ka samu dama, ko zuwa gobe in Allah ya kaimu ka zo gida, ina son mu yi wata muhimmiyar magana da kai" Viper ya jinjina kai, Baba ya ce "Bari a kawo abinci mu ci baki ɗaya" Al'amin ya ce "Baba ayi mini uzuri dan Allah, ana jirana ne, ayi mini afuwa" ya fita ya sanya takalmansa ya tafi. Rarrashin Abbu suka din ga yi, saboda yadda jikinsa yayi sanyi, dan gani yake yi, kamar da wani abun a ran Al'amin haryanzu, duk da ya san halinsa farin sani, ba kowane lokaci ake iya gane yanayin sa ba. *** Washegari Nabila ta kira Abbu a waya, domin ta ji ya ake ciki, ko Al'amin ɗin ya saukko?. Abbu ya ce "Kin san ɗan nawa hukuma ne sai da rarrashi, ya ce dai ya wuce, amma bai tsaya mun ci abinci tare ba, yau dai ina jiransa, ina son ya zo zamu yi magana da shi, idan ya zo kin ga sai na ɗan ƙara saka ran ya saukko ko?" Sai ya ba wa Nabila tausayi, ta ce "Abbu ka kwantar da hankalinka, Viper yana sonka haryanzu, shi ba abubuwan da ka yi masa ne suka dame shi ba, korar da ka yi masa ce kawai ta tsaya masa, amma tun da ya ce maka ya yafe, ya yafe ɗin ne, dan Allah ka kwantar da hankalinka Abbu, idan ma bai zo ba na yi maka alƙawarin kawo maka shi har gida in sha Allah" Abbu ya ce "To shikenan, na kwantar da hankalina, Allah ya saka miki da alkhairi" "Amin bakomai Abbu, sai anjima" Shahida ita tayi girke-girken zuwan Al'amin, Rahila na gefe tana kallonsu, sai yan surutai take da ƙanan maganganu saboda ƙwaƙwalwarta ta riga ta taɓu, amma har aka yi sallar magariba Viper bai zo ba. Hakan ya ƙara sanya Abbu karaya nesa ba kusa ba, domin kuwa yana da muhimmiyar magana da yake so su yi. Shahida tayi ta ci gaba da bashi haƙuri, amma a washegari ma still babu Viper, babu dalilinsa, tun Abbu yana sanya ran ganinsa har ya sare. **** Viper yana ganin kiran Nabila, amma ya shareta. Message ta turo masa "Ka ɗaga wayata, is an emergency" Sai da ta kusa katsewa, sannan ya ɗaga yana hura hanci. "Vi wai dan Allah meyake damunka ne, kai mutum nawa ka yi wa laifi kai ko neman yafiyar ma baka yi, kai shikenan komai naka babu sauƙi, Abbu ya nemi afuwarka, amma ka yi burus, ya ka ke so yayi ne?. Idan shi ma ya mutu sai ka huta, ni dai nayi iya yi na, sauran na bar wa Allah, ban san ya zan yi maka ba kuma, Abbu yana Asibiti ya yanke jiki ya faɗi, ana addu'a Allah ya sa ba ɓarin jikinsa ne ya taɓu ba, yana ta kirana a waya, yana gaya mini kamar baka yafe masa ba, ya nemi ka je ka ƙi zuwa, to yanzun ma Viper idan ka yi ra'ayi ka je, idan ba ka yi ra'ayi ba shikenan, ni fara gajiya da halinka" Ba tare da ta kashe wayar ba, ya ajiye wayar, yana duba agogon hannunsa, sauran awa ɗaya ya shigo garin Kano, ranar da ya baro wurinsu, aka tura shi Jos, kuma yana sane da kiran da Abbun yayi masa, dajin da yaje ko network babu. Sai dai ƙirjinsa ya din ga bugawa, hankalinsa yayi mummunan tashi, ya shiga fargaba da zullumin rasa abu mai muhimmanci a rayuwarsa karo na babu adadi. Ayshercool 08081012143 98 Shiru yayi yana dubanta, domin ya tabattar idan da gaske take, sai dai yanayin fuskarta ya tabattar masa da gaske take yi ba wasa ba. Basarwa yayi ya ce Shikenan su tafi, amma deep down ya ji zafin abin da ta yi masa nesa ba kusa ba, he wish 'yar madararsa tana raye, da ya san ita ba zata watsa masa ƙasa a ido ba, kamar yadda Nabila ta yi yanzu ba. Dan rashin kunya, su na tafiya a hanya kuma, ta na yi masa hira da surutu, ganin ya yi mata banza, ya sanya ta ja bakinta ta tsuke, kuma ta tabattar fushi ya yi. A hanya ya sauka, ya bar ta da Joseph, ya mayar da ita gida, shi kuma yayi nasa wuri. **** Washegari da yamma, Abba yana gidan gonarsa, yana office ɗin sa, ana ta fitar da ƙwai na kaji, da na sauran tsuntsaye ƙaton gidan gona ne sosai da sosai, gidan gonarsa na cikin manyan gidajen gona da yake fitar da ƙwai, har maƙwabtan garuruwa. Da su kansu kajin da kifaye, ban da sauran dabbobi. Masinja ya sanar da shi ya yi baƙo, Abba ya ce a shigo da shi. Mintuna kaɗan aka buɗe ƙofar Office ɗin aka shigo, ajiye biron hannunsa ya yi yana kallon Viper. Viper ya yi sallama, Abba ya amsa a hankali yana ci gaba da kallonsa. Ya ƙaraso ya tsaya, ya gaida major cikin girmamawa kamar yadda suke yi a tsakaninsu masu ɗamara, hakan ya tabattar wa Major akwai wani abu tattare da baƙon nasa. Ya bashi dama ya zauna. Viper ya ce "Duk mun taɓa haɗuwa ba na da tabbacin ko ka gane ni, amma bari na sake gabatar maka da kaina, sunana Al'amin Ibrahim, wanda 'yar ka Nabila ta tsayawa a kotu, kuma mijin 'yar uwar Nabila da Allah ya yi wa rasuwa" "Mijin wadda ka kashe dai, da babanta bai san ciwonta ba ya ɗauketa ya aura maka. Ta yaya zan kasa ganeka, da ka ɓata mini shirina na shekara da shekaru ka ɗauki Nabila ka haɗata da babanta, mutumin da bai martaba rayuwar uwarta da ta 'yar uwatta ba har ya iya aura maka ita ka kasheta". "Ba ni na kasheta ba, kamar yadda kotu ta tabattar kuma ta wanke ni, ina roƙonka saboda Allah, kar laifin da ba namu ba ya shafe ni da ni Nabila, mussman ma ita. Makamancin abin da ya faru da Jauhar, irinsa ne a rayuwata, da ya jefa ni cikin ƙaddara. Duk wannan mummunar rayuwa da nayi, ta samo asali ne daga rashin samun ingantaccen bangon da zan jingina rayuwaya da shi, sai da ƙaddara ta saka aurena da Jauhar, ba zan taɓa mantawa da ita ba har duniya ta naɗe, kuma ban kashe jauhar ba. Kamar yadda kotu ta tabattar, duk da na fuskanci mutum ne kai irina, muna amfani da ƙwaƙwƙwarar shaida da muka gani a zahiri ne, ba dan haka ba, ba zan so na baka wata gamshashshiyar hujja da shaida da zata tabattar maka da Nabila a kan dai-dai take, kamun da aka saka ɗanka yayi mini ba bisa ƙa'ida bane ba. Da fari hukumar'yan sanda ce ta bashi umarnin, daga baya kuma an bashi maƙudan kuɗi dan ya kama ni, hakan ya sanya ya din ga ɓata Nabila a idonka. Duk ban gaya maka wannan abun da raba maka kan iyalinka ba, roƙonka kawai nake yi, ka daina fushi da Nabila, duk da ganin mahaifinta da ta yi, a duniya ba ta da wani wanda ta shaƙu da shi take ƙauna sama da kai. A madadinta ina mai ƙara baka haƙuri, domin kuwa na san duk ni ne silar komai, amma dan Allah na roƙe ka, ka yi haƙuri ka yafe wa Nabila da mahaifinta, ci gaba da fushi da ita, zai kua jefa rayuwarta a cikin damuwa" "Ka gama?" Major ya yi maganar yana kallon Viper. Viper ya yi shiru bai ce komai ba. "Na ji na kuma gode, amma ka tashi ka tafi, ka ɓata ruwa ba domin ka sha ba, ka ɓata mini haɗin kan iyali" "Abba ban ɓata maka kan iyali ba, son abin duniya ne ya rinjayi Nasir, ya ƙara ta'azarra al'amarin, ina sake baka haƙuri, saboda Nabila kar azo ta shiga wani halin" ya na gama maganar ya tashi tsaye ya fice daga ofishin. Bayan fitarsa Major ya yi shiru yana kallon ƙofar da ya fita, da nazartar maganganun da ya yi. Gaba ɗaya Viper ya daina kiran Nabila a waya, ita ma kuma ba ta neme shi ba, hakan ya ƙara tunzura shi, ganin yadda ta watsar da shi gaba ɗaya. Major ya so ya yi wa Nabila maganar zuwan Viper in da yake, amma yayi mata shiru ya rabu da ita. ***** Satin awon Ramma ya zagayo, Nabila ta je ta ɗauki ramma, suka je asibiti. Aka yi mata awo aka duddubata, komai nata lafiya ƙalau. Su ka tsaya suka yi sayayya, suka tafi prison. Ramma sai murna take yi tana jin daɗi za ta ga Abdul. Saboda yadda Nabila ta zama popular yanzu, duk in da ta shiga an santa, tana samun alfarma, yau ma har ciki aka shiga da su. Aka je aka fito musu da Abdul, yana ganin ramma ya saki murmushi, ita ma murmushin ta sakar masa, ta miƙe tsaye ba tare da ta san ta miƙe ba. Nabila ta ce "Bari na baku wuri, idan kun gama ma gaisa" ta fita waje, bai damu da gandiroban da yake wurin ba, ya rungume abar sa. Ta ce "Doctor ya jikin ka warware?" "Inyee an daina gantsara mini sunana,  Abdul yasar" Ta saki murmushi ta ce "Ko dan saboda wannan ai yakamata na fara saye sunan" tayi maganar tana nuna masa cikinta, da ya kai watanni shida ya fito sosai. Murmushi yayi ya zira hannunsa cikin hijjabinta, ya shafa cikin nata. "Ina fatan dai wurin awon babu wata matsala da babyn namu?" Ta ce "Anty Nabila tana kula da ni sosai, tana kai ni awo" "To ki na cin abincin da shan maganin dai ko?" Ta jinjina kai ta ce "Eh, kawai dai ina son na ga ka fito ne, ina cikin damuwa tsareka a wurin nan" Ya kalli wurin ya ce "Kar ki damu, ai na riga ma saba kuma ba wata wahala nake sha ba your excellency, kewarki nake tayi ne dai kawai, amma yaya zasu bar mu mu cigaba da zaman aurenmu?" Ta rausayar da kai, ta ce "To gashi nan dai, ban san ya ake ciki ba, basu sake cewa komai ba. Ina son in roƙi Anty Nabila, ta ɗan ƙara lallaɓa mini su, amma nauyinta nake ji". Ya ja hannunta suka zauna, ya ce "Ni zan roƙeta, ko sake durƙusawa zan yi a gabansu na basu haƙuri, ni dai su bar mini ke babyna, da ke jaririnmu mu rayu tare ko Rahamana?" Ta jinjina masa kai, ta numfasa ta ce "To yaya yanayin abincin kana samu ka ci kuwa?" "Eh mana, komai nawa normal kawai dai ina tsare ne, ki kwantar da hankalinki, ki rainar mana babynmu, ina fatan lokacin da zan fito yayi dai-dai da lokacin da zaki haihu, a karɓi haihuwar nan da ni. Na so ni zan kula da ke ayi rainon cikin nan da ni" "To yaya zamu yi, kana naka Allah ya sa shi ne dai-dai, Allah ya fito mini da kai lafiya" Abdul ya dafa kafaɗarta ya ce "Naki ne ni?" Ta jinjina masa kai cikin jin kunya tana murmushi. "Naki ne ni rahama, ƙaddararmu ce ta zo mana a hagunce, amma mun gode masa Allah ya sassauta mana, ya sanya su barmu mu yi rayuwarmu ta aure" Ta ce "Amin, bari ta zo ku gaisa, mu tafi, na san yanzu za su ce mu tafi" Ya marairaice ya ce "Haba dai, kwata-kwata yaushe ku ka zo, ban gaji da ganinki ba, yayi maganar yana sumbatar goshinta. Gandiroba ya ce "To sharokhan baban soyayya, lokaci yayi" Abdul ya yi murmushi ya ce "Ai shi sharokhan na shi film ne, ni kuwa soyayya ce ta zahiri, dan haka ni na fi shi ma" yayi maganar yana dariya. Nabila ce ta dawo, suka gaisa da Abdul, sai dai da ta ga farinciki a fuskokinsu, sai ta ji daɗi. "Ina godiya sosai da sosai, rahama ta gaya mini yadda ki ke kula mini da ita da babyna, Allah ya saka miki da alkhairi" Nabila ta ce "Amin, ai yi wa kai ne, rahama ƙanwata ce, ina jin daɗin ganinta cikin farinciki. Nayi mamakin yadda aka yi ka yi mata laifi kamar wannan kuma ka iya dasa soyayyarka a cikin zuciyarta. Meye sirrin ne?" Yayi murmushi ya ce "Ita zaki tambaya ai" Ramma ta harare shi ta ce "Ba wani sirri, ban da faɗa me ka iya?" "Soyayya" ya bayar da amasa kai tsaye, da sai da ramma ta ji kamar ta nutse. Suka yi dariya, ya sake cewa Nabila "Dan Allah na ga kamar ke kina tausaya mana, dan Allah ki rarrashi mama, ki ba ta haƙuri su bar mana aurenmu dan Allah" Nabila ta sauke numfashi ta ce "To bani da ta cewa ne, idan na matsa yayanta hayayyaƙo mini zai yi, amma zan lallaɓa ta ɓangaren mama na cigaba da shawo kanta, in sha Allah komai zai wuce" Ya ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya saka da alkhairi. Idan da wani abu ko kuɗi sun yi kaɗan, ayi mini magana" Nabila ta ce "Kai wane irin kuɗi sun ƙare, wannan maƙudan kuɗi har haka, akwai kuɗi sosai in sha Allah ba wani abu" Ya ce "To shikenan, muna godiya sosai barrister, babyna sai yaushe kuma?" Ramma ta galla masa harara, amma bai fasa ba, ya riƙe hijjabinta, ta waiwayo ta fizge ta na murguɗa masa baki. Shafar sumar kansa ya yi, yana dariya, suka fice ita da Nabila. Suna tafe a hanya, Nabila ta ce "Ramma har mamaki ku ke bani da ke da Abdul, dan Allah me Abdul ya yi miki, har ki ka fara sonsa, duk da girman laifin da ya aikata miki?" Ramma ta jinjina kai ta ce "Na san da yawa ba za su fahimce ni ba, za a zata ko kwaɗayin wani abu ne na hannunsa, ko kuma wani abu nake yi wa, wanda ni har muka rabu ban san menene auren ba, kawai dai ina jin daɗin shiryuwar sa a dalilina. Kuma yana da wasu nagarta, wanda shi kansa bai san yana da ita ba. Da ya samu isashshiyar tarbiyya, ba zai yi wasu abubuwan ba. Ya nuna tsantsar nadamarsa, gani nake idan na rabu da shi, zai iya koma wa ruwa, duk da da gaske, yake tuba a kan abubuwan da yake aikatawa. A matsayin ya aureni, ya tabattar mini da ya aure ni, babu irin zagi da rashin mutuncin da ban yi masa ba, amma ko a jikinsa, bai taɓa damunsa ba, kawai zai yi abin da ya ga dace yayi domin ya kyautata mini, ko na yaba ko na kushe bai dame shi ba. Sannan daga halayensa masu kyau, yana da tausayi da taimako, mutum ne mai kyauta ta ban mamaki, kuma ya san aikinsa sosai da sosai, ina duba wannan abubuwan ne, amma ni kaina na san ta wani ɓangare kamar ban kyauta wa kaina da mama ba" Nabila ta ce "Kar ki ce haka, wannan shi muke kira da jarrabawa, Allah ya jarabce ka ya ga yaya zaka yi? Bar ganin Abdul ba ya ji, wallahi sai ki ga saboda yawan kyautarsa da taimakonsa, ya sanya Allah ya din ga ji da shi, maybe shiyasa ya sanya tsautsayin nan a tsakaninku, domin ya rabauta ya tuba, yadda ya daina zina within shot period of time da ku ka zauna, ya cancanci a yaba masa daga ke har shi, ina fatan Allah ya tabattar da alkhairi a zamanku, ya sanya sanadin shiriyar sa kenan, idan Allah ya tabattar da zamanku, ki yi ƙoƙari ki rufa masa asiri, ki zauna da shi da zuciya ɗaya, ki yafe masa". Ramma ta ce "In sha Allah Anty, na gode sosai da sosai, Allah ya nuna mana aurenku ke ma, da Yaya Al'amin" Nabila ta kalleta ta ce "Da wa? Wannan yayan naki ai sai Jauhar ɗin, Allah ya bashi mace ta gari dai ba Nabila ba" Cikin mamaki Ramma ta ce "Amma Anty Nabila saboda me? Wallahi yana da kirki, yana da faɗa ne dai kawai" "Wasu dalilai rahama, ki manta kawai, ba soyayya muke yi ba dama, kawai dai nima yayananne" Jiki a sanyaye ta ce "A'a shi sonki yake yi" "Yaya aka yi ki ka sani, shi ya gaya miki?" "Ni a wa zai gaya mini, bai gaya mini ba, amma wasu lokutan irin kallon da Abdul yake yi mini, yake yi miki. Idan mutane sun kai goma a wuri, duk wanda zai yi magana ba zai damu ba, amma da kin fara magana, zai tattara nutsuwar sa da hankalinsa a kanki. Ko wani abin ki ke yi daban, yana kallonki ta ƙasan idonsa" Kwashewa da dariya Nabila ta yi, ta ce "Kai rahama, haka ki ke saka masa ido kina kallonsa, ke duk a ina ki ka san hakan shi ne so?" "Wurin doctor, amma Wallahi yana sonki" "Daina rantsewa rahama, Viper mace ɗaya tak yake so a duniya, kuma yanzu ba ta raye, babu kuma macen da za ta iya maye gurbinta, dan haka ki manta kawai" Rahama ta ce "Shikenan, tun da kin ce haka, amma ai kamarku ɗaya ita, kema yana sonki, ina ga dai ke ca ba kya sonsa kawai" Rahama tayi maganar cikin sanyin jiki sosai, dan tana son ta ga sun yi aure, dan sun dace sosai. **** Abubuwa suka din ga damun Major, game da maganganun da Viper ya gaya masa, sai ya kasa haƙuri, ya kira Nasir ɗakinsa. Ya dube shi sosai sannan ya ce "Nasir tambayarka zan yi, kuma ina so ka ji tsoron Allah, ka gaya mini gaskiya" Ya ce "To Abba in sha Allah" "Waye ya saka neman yaron nan da Nabila ta kare?" Ya numfasa ya ce "Abba maitaimakin CP ne" Abba ya ce "Da kuma wa?" "Shikaɗai ne Abba" "Gaskiya na ce ka gaya mini, waye ya baka kuɗi a matsayin cin hanci, ya ce lallai ka nemo shi? Kar ka yi mini ƙarya, ka san nima tsohon ma'aikaci ne" "Ba kuɗi aka bani ba, senator ma'aruf Indabo ne" "A kan me zai saka ka nemo masa wani ɗan daba, menene alaƙarsa da ɗan daba yana sanata?" Nasir ya girgiza kai ya ce "Nima ban sani ba Abba" "Baka sani ba, kawai ka karɓa ka fara yi, Nasir idan baka ji tsoron Allah a kan aikinka ba, a tsiyace zaka shekara talatin kana wahala, ka gama aiki ka zama abin tausayi. Na fara yadda wasu abubuwan kai ka ta'azzara su, kamar Nabila ta fika gaskiya". "Abba mutumin fa ɗan daba ne, da yake zubar da jini, da aikata miyagun laifuka" Major ya ce "To meyasa ba ku nemi kama shi a kan laifin da yake aikatawa ba, wani zai ja ka gefe ya kuma tunzuraka, ba tare da ka san abin da ya haɗa su ba, Nasir ka san aikinka kuwa? Kaga tashi ka je kawai jeka" Ya buɗe baki zai yi magana major ya ce "Jeka ba zan sake magana da kai a yanzu ba, ina dai tunatar da kai muddin ka gauraya halal ɗinka da haram, babu in da zaka je wallahi. Kuma ka ji tsoron Allah, kar masu ƙarfi su din ga amfani da kai, a kan marasa ƙarfi, saboda kana saka wannan kakin lokaci ne" Sosai kunya ta kama Nasir, saboda yadda asirinsa yake nema ya tonu, na ya karɓi cin hanci, ya din ga matsawa Nabila da ƙoƙarin daƙileta a kan nata aikin. *** Cikin dare hasken farin wata ya gauraye ko ina, Viper na tsaye a bakin window, yana shan sigari, hannunsa ɗaya yana kallon wayarsa, kwanaki shida kenan rabon da su yi waya ko ya sanyata a idonsa, babban mamakin da ta bashi, yadda ƙiri-ƙiri ya nuna mata yayi fushi, amma ko ta sake neman sa. Haka kurum ya ji ya ƙara fusata. Ya harɗe ƙafarsa, yana ci gaba da shan sigarin, kawai sai watarana ta faɗo masa, Jauhar ta tsare shi a gida, ta hana shi fita ko ina, kuma ta bashi kara uku na sigari kawai. Cikin dare ta yi bacci, ya tashi ya fita tsakar gida, ya shiga banɗakin tsakar gida, ya sha son ransa, ya daɗe hayaƙin ya ragu, sannan ya koma ɗakin ya kwanta. Ashe tun da ya tashi ya fita, tana kallonsa, yana kwanciya ta tashi ta matso kusa da shi, ta saka hannu ta matsa bakinsa, ta sinsuna, dan ta tabbatar masa ta san me yayi, ba ta ce masa komai ba, ta juya ta kwanta. Kamar wanda ta kama yana alfasha, yayi tsuru-tsuru, ya rasa me ma zai ce mata, kawai ya basar. Aka jima yana ƙoƙarin ya rungumeta, dan ya mantar da laifin da yayi, ta tashi ta bar masa gadon, ta yi alwala ta tayar da salla. Asubar fari ba ta tashe shi ba, yaje masallaci ya dawo, a gida yayi azkar, ya din ga 'yan kame-kame, amma taƙi kula shi, har gari ya waye, sai da ya gaji ya ce "Ni fa guda uku na sha kawai ba da yawa ba" Ta kalleshi ta ce "Me fa?" "Sigarin" ta ɓata fuska ta ce "Hakan ya tabattar mini da zaka iya cin amanata wataran, ka yi abu ban sani ba" Ya girgiza kai ya ce "Ai uku ce kawai ba wata mai yawa ba, ki ke wani haɗe rai " "To Allah ya baka haƙuri, na ga kamar na matsa maka" daga haka ta ci gaba da sabgarta. Ranar ba ta hana shi fita ba, ya zauna bai fita ba, ko zata huce, har da yi mata aikin gida, amma ya kasa cewa ta yi haƙuri, ta tabbatar da ya sha jinin jikinsa, duk ya damu, amma ya kasa ba ta haƙuri. Duk sallolin ranar a jam'i ya yi su. Kafin ya dawo daga sallar isha'i, ta sha kwalliya, yana dawowa ta rungunmi abin ta, kamar ba fushi tayi da shi ba, iya punishment ɗin nan da tayi masa, sai da ya ji kamar ya shekara a prison. Jauhar akwai iya dealing ta cikin ruwan sanyi, a lokacin babu wani abin da yake shakka irin yi mata laifi, saboda ta riga ta sanshi, ciki da bai ta san hanyoyin hukunta shi. Sakin guntuwar sigarin yayi, ya koma ɗaki ya kwanta ya cigaba da tunaninta. Da haka wani nannauyan bacci ya ɗauke shi, sai dai kasancewar da ita ya kwanta a ransa, sai ya din ga mafarki da ita, mafarki mai cike da shauƙi da nishaɗi irin na ma'aurata. "Master salla fa, zaka rasa sallar asuba." tayi maganar tana shafa sumar kansa. Ƙanƙameta ya ƙara yi, yana tura kansa cikin wuyanta, da yake fitar da daddaɗan ƙamshin turaren da yake matuƙar son jin tashinsa daga jikinta. "Viper wai ina zaka shiga a cikin pillown nan ne? Wai ko dai ka sha wani abu bamu lura ba, tun ɗazu fa muke tashinka, ka tashi mu yi salla dan Allah" A hankali ya motsa, ya buɗe idonsa ya ga hasken fitilar solar, ya haske ɗakin, sai a lokacin ya lura da ya ƙanƙame pillow. Yayi miƙa tare da yin salati, ya kalli liti da yake tsaye a kan sa ya ce "Akwai gas ne?" "A'a ɗan kaɗan ne sosai, sai an yi refiiling ma zamu iya dafa karin kumallo". "Ɗora mini ruwa, ku yi sallarku zan yi wanka" "Wai Viper meyake faruwa ne kwana biyun nan, ko ka fara dawowa bil adama ne? Ni ina cewa ka yi wa addini hidima meyake faruwa" Ashar Viper ya yi masa, ba shiri liti ya ce "Allah ya baka haƙuri, ya ƙara lafiya" Walid kuwa dariya yayi, ya ce "Allah ya ƙara, uban son jin ƙwaƙwaf". Bayan sun karya Baba ya kira Viper a waya, ya ɗaga suka gaisa, ya ce "Aminullahi, dan Allah idan baka komai zuwa azahar ina son ganinka" "To Baba in sha Allah zan zo, nan gidan zan zo na same ka?" "Eh dan Allah" "Zan zo in sha Allah" "Yauwwa Allah ya yi maka albarka" Viper ya amsa da Amin. Ɓangaren Nabila ita ma kwanaki bakwan nan da suka yi, ba sa magana da Viper, abin ya dameta, ƙishirwar son ganinsa ta addabeta, ga ayyuka sun fara yi mata yawa, 'yat shaharar da tayi ta kwanan nan, ya sanya take ta samun cases ko ta ina. Ban da masu nuna suna sonta, manyan mutane da suke sonta da aure. Yau da mafarkin da tayi ta tashi a zuciyarta, mafarki tayi da mai kama da ita, wadda take da tabbacin jauhar ce. Tana nuna mata inuwar mutumin da yake ɗaure cikin sarƙa a baya, yanzu babu sarƙar, sai dai daga yanayin inuwar tasa, kamar a galabaice yake, duk da babu sarƙar sai tangaɗi yake yi. Tana murmushi ta cigaba da nuna mata shi, ta nufi in da take nuna mata, sai dai da ta waiwaya ba ta ganta ba, tana ƙoƙarin ƙarasawa in da mutumin yake, kawai ta farka daga baccin. A hankali ta furta Viper, a gurguje ta shirya, tayi ta trying lambarsa, amma yaƙi ɗagawa, ta din ga jin ko me zai yi mata, yakamata ta kira shi, ta ji ya yake. **** Ko da Viper ya je gidan su Jauhar, ya tarar da motoci a ƙofar gidan, bai damu da ko me ake yi ba, ya kira Baba ya ce masa gashi nan yana ƙofar gida. Baba ya ce ya shiga kawai, ya ƙarasa ya shiga, babu wanda ya kula a mutanen gidan, sai hafsa da suka gaisa ya shiga ɗakin Baba. Alhaji mu'azzam ya tarar, da Abbu, da kuma shi kansa Baban. Gefe ya samu ya zauna a ƙasa ya gaishe su, sai dai da ya zo kan Abbu kamar an yi masa dole, haka ya gaishe shi. "Ya gida ya ƙoƙarin Kuma?" Baba ya tambayi Viper. "Lafiya ƙalau Alhamdilillah" "Ina yan uwan naka?" Viper ya ce "Su na gida, nikaɗai na zo". Baba ya ce "babu laifi, Al'amin" "Na'am Baba" "Na san zaka yi mamakin kiranka da muka yi, babu tsammani da wuri haka. To bakomai bane ya janyo, Nabila ta same ni, tayi mini wata magana ne, kuma nima naga hakan yakamata, duba da yadda abubuwa suka wakana. Al'amin su iyaye, ba a fushi da su, kuma duk lalacewarsu iyaye ne, balle babu lalacewa a cikin iyaye, yakamata ka sasanta da mahaifinka, yanzu ina jauhar, ina mahaifiyarka, ina ɗan uwanka, ko da kuɗi ba zaka sake ganinsu a gidan duniya ba. Dan haka ka yi haƙuri, mun san mu masu laifi ne a wurinku, amma ku yi haƙuri a yafe ya wuce dan Allah ba dan halinmu ba". Viper ya yi shiru, kamar mai nazari amma bai ce komai ba. Abbu ya ce "Al'amin, nauyinka da nake ji, ya sanya na kasa nemanka gaba da gaba na nemi afuwarka, na san in dai dan halina ne, da abin da na aikata maka, ba zaka sake kallona a matsayin mahaifi ba, amma ba dan halina ba domin Allah. A ƙaddarar rayuwarmu, na ɗauki darasi da dama, daga illar da mutum zai yi wa rayuwarsa, shi ne auren mace domin buƙatarsa kawai, ba tare da tunanin abin da gobe ka iya haifarwa ba. Duk da ni a zatona dan gobenku na auri Rahila, amma ta ci amanata, kuma nima na san da laifina na rashin bibiya da tantance abin da take ɗora ni a kai, amma dan Allah ka yi haƙuri Al'amin, ka yafe mini ka dawo gida mu yi rayuwa a ɗan abin da yayi mini saura na rayuwata" Alhaji mu'azzam ya ce "Viper, ka yi haƙuri dan Allah, duk wani abu da ya faru, ya wuce tun da bawan Allah nan shi yayi silar zuwanka duniya, kuma wani abin idan bai yi maka ba, wani yayi maka, yana cikin tashin hankali da damuwa sosai" Viper ya numfasa ya ce "Ko a baya ni ban ƙi Abbu ba, ina matuƙar ƙawazucinsa da son kasancewa tare da shi, Abbu shi ne ya ƙi ni ya kore ni, amma tun da yanzu ya nemi na dawo shikenan, ya riga ya wuce. Amma ni a yanzu na girmi zaman gida, ba zan iya rabuwa da su Walid ba, sai na tabattar da rayuwarsu ta inganta suma, kamar yadda suka rayu da ni lokacin da kowa yake mini kallon mara amfani. Kuma idan na koma gidan nan, zai iya cigaba da haddasa husuma, wanda ni kuma bana fatan hakan". Abbu ya ce "Hakan ma na gode Al'amin, Allah ya ƙara shirya mini kai, dan Allah idan ka samu dama, ko zuwa gobe in Allah ya kaimu ka zo gida, ina son mu yi wata muhimmiyar magana da kai" Viper ya jinjina kai, Baba ya ce "Bari a kawo abinci mu ci baki ɗaya" Al'amin ya ce "Baba ayi mini uzuri dan Allah, ana jirana ne, ayi mini afuwa" ya fita ya sanya takalmansa ya tafi. Rarrashin Abbu suka din ga yi, saboda yadda jikinsa yayi sanyi, dan gani yake yi, kamar da wani abun a ran Al'amin haryanzu, duk da ya san halinsa farin sani, ba kowane lokaci ake iya gane yanayin sa ba. *** Washegari Nabila ta kira Abbu a waya, domin ta ji ya ake ciki, ko Al'amin ɗin ya saukko?. Abbu ya ce "Kin san ɗan nawa hukuma ne sai da rarrashi, ya ce dai ya wuce, amma bai tsaya mun ci abinci tare ba, yau dai ina jiransa, ina son ya zo zamu yi magana da shi, idan ya zo kin ga sai na ɗan ƙara saka ran ya saukko ko?" Sai ya ba wa Nabila tausayi, ta ce "Abbu ka kwantar da hankalinka, Viper yana sonka haryanzu, shi ba abubuwan da ka yi masa ne suka dame shi ba, korar da ka yi masa ce kawai ta tsaya masa, amma tun da ya ce maka ya yafe, ya yafe ɗin ne, dan Allah ka kwantar da hankalinka Abbu, idan ma bai zo ba na yi maka alƙawarin kawo maka shi har gida in sha Allah" Abbu ya ce "To shikenan, na kwantar da hankalina, Allah ya saka miki da alkhairi" "Amin bakomai Abbu, sai anjima" Shahida ita tayi girke-girken zuwan Al'amin, Rahila na gefe tana kallonsu, sai yan surutai take da ƙanan maganganu saboda ƙwaƙwalwarta ta riga ta taɓu, amma har aka yi sallar magariba Viper bai zo ba. Hakan ya ƙara sanya Abbu karaya nesa ba kusa ba, domin kuwa yana da muhimmiyar magana da yake so su yi. Shahida tayi ta ci gaba da bashi haƙuri, amma a washegari ma still babu Viper, babu dalilinsa, tun Abbu yana sanya ran ganinsa har ya sare. **** Viper yana ganin kiran Nabila, amma ya shareta. Message ta turo masa "Ka ɗaga wayata, is an emergency" Sai da ta kusa katsewa, sannan ya ɗaga yana hura hanci. "Vi wai dan Allah meyake damunka ne, kai mutum nawa ka yi wa laifi kai ko neman yafiyar ma baka yi, kai shikenan komai naka babu sauƙi, Abbu ya nemi afuwarka, amma ka yi burus, ya ka ke so yayi ne?. Idan shi ma ya mutu sai ka huta, ni dai nayi iya yi na, sauran na bar wa Allah, ban san ya zan yi maka ba kuma, Abbu yana Asibiti ya yanke jiki ya faɗi, ana addu'a Allah ya sa ba ɓarin jikinsa ne ya taɓu ba, yana ta kirana a waya, yana gaya mini kamar baka yafe masa ba, ya nemi ka je ka ƙi zuwa, to yanzun ma Viper idan ka yi ra'ayi ka je, idan ba ka yi ra'ayi ba shikenan, ni fara gajiya da halinka" Ba tare da ta kashe wayar ba, ya ajiye wayar, yana duba agogon hannunsa, sauran awa ɗaya ya shigo garin Kano, ranar da ya baro wurinsu, aka tura shi Jos, kuma yana sane da kiran da Abbun yayi masa, dajin da yaje ko network babu. Sai dai ƙirjinsa ya din ga bugawa, hankalinsa yayi mummunan tashi, ya shiga fargaba da zullumin rasa abu mai muhimmanci a rayuwarsa karo na babu adadi. Ayshercool 08081012143 99 Har zai sake bin Nabila a waya, kawai ya tuna yadda ta ɗaga masa murya, ya ɓata masa rai ƙwarai da gaske, kawai ya fasa kiranta ya kira Walid a waya. Walid ya ɗaga ya ce "Mazaa ka ƙaraso ne?" "Ina hanya, yarinyar nan ta kira ni ta ce Abbu yana Asibiti, ka je ka bincika mini" Cikin tashin hankali Walid ya ce "Asibiti kuma? Wane Asibitin? Nabila ce ta gaya maka?" Viper ya ce "Ban san wane asibitin ba ne, ka tambaya mini kawai ka bincika mini, idan ma mutuwa yayi kawai ka gaya mini ba wani abu" "Ahh no, in sha Allah yana raye, tambeyata yana wani Asibitin?" "Manta da ita, ka duba mini kawai" "Ok yanzu kuwa in sha Allah" Allah ya sa yana wurin shayinsu, dan haka ya tashi ya tafi gidansu Viper, ya rasa wa zai aika gidan, Shahida ta fito hannunta riƙe da leda. Gaida Walid tayi, ya amsa. Ya ce "Ya ake ciki, mai zamani ya kirani, ya ce an kwantar da Abbu a asibiti na zo na bincika masa" Ta kalle shi ta ce "Dan Allah da gaske shi ne ya ce ka zo ka bincika masa?" "Eh mana, yanzu muka gama waya da shi ma" Ta ce "Damuwar yaƙi zuwa, ya sanya Abbu ya faɗi, Abbu yana ta roƙon ya yafe masa amma yaƙi damuwa da hakan" tayi maganar tana share hawaye. "Kin ga ki daina kuka, ya gaya mini ya zo sun haɗu a gidansu jauhar, har Abbu ya buƙaci ya zo su yi magana, wai wani wuri aka tura shi a Jos, wurin ko network babu, shiyasa bai zo ba, amma wani Asibitin ne?" "Can zan je yanzu, in da muke ganin likita ne" suka rankaya suka tafi, yana ta bata haƙuri. Ga mamakinsa a can suka tarar da Nabila da Sumayya, har da Murtala abokin aikin Sumayya. Suka gaisa da Nabila, cikin damuwa Nabila ta ce "Oga walid, Vi ba ya kyautawa ko kaɗan, wane irin abu yayi haka fisabilillahi?" "Allah ya baku haƙuri, mun gode sosai da kulawarku a kan babanmu" Nabila ta ce "Ai ba dan shi muka yi ba, dan Allah muke yi, dan kuma ƴar uwata, ayi mutum sai zafin rai, komai ba zai yi a hankali normal kamar kowa ba" Walid ya ce "A'a fa, muna fa kawar miki da kai duk da haka, kar ki ƙure mu Barrister, ba fa haka Jauhar take yi mana ba" Nabila ta ce "Taɓ ai ita wannan, idan ana ganin ɗan aljanna a duniya sai a nunata, ina zan iya, wataran sai baƙin ciki ya kasheni. Kayi ta yi wa mutum magana, amma ya gagara responding ma, ya ƙame yana harararka" Yayi murmushi ya ce "Yanzu yaya mai jikin?" "An yi masa alluran bacci ne, an ce mu jira kar wanda ya shiga sai bayan 2hours tukuna, amma jikinsa Alhamdilillah. Nima sumayya ce ta gaya mini ba shi da lafiya, sun yi waya da wannan sistern ta shi" tayi maganar tana nuna Shahida. Tun da Nabila ta fara magana Shahida take kallonta, a nan take ƙara gano bambancin Jauhar da Nabila, Jauhar ba zata taɓa reacting a hasale haka ba, komai girman laifin da ya yi mata kuwa. Wannan kuma a tsaye take, ba ta ɗaukar komai a hankali. Har mamakin yadda take faɗar maganganu a kan yayanta take yi. Viper ya sake kiran Walid a waya, "Ya mutu ne ko kuwa?" "A'a lafiyarsa ƙalau, yana samun kulawa ta musamman" "Walid, dan Allah kar ka ɓoye mini, ba wani abu ka gaya mini kawai, ba yau na saba ji ba" yayi maganar haɗe da wani irin wahalallen numfashi na razani. "A'a wallahi da gaske nake yi maka, muna tare da Nabila ma, ko na baka ta tabattar maka" "A'a, tura mini adress ɗin, yanzu zan ƙaraso in sha Allah" Shahida dai gefe ta koma ta zauna, tana ta kallon Nabila, babu yadda za ayi ka ce ba Jauhar ba ce ba. "Haryan ƙoƙarin tantancewa ki ke yi ne?" Ta ji maganar Walid unexpected. Ta ce "Eh wallahi, haryanzu na kasa yadda, abin mamaki yake bani" Yayi murmushi ya ce "Haka ne" Sai da aka yi kusan awanni uku, sai ga Viper, tamkar an hankaɗo shi, ya yi duhu sosai da sosai, idanunsa jawur, yana zuwa Walid ya miƙe ya nufe shi. "Walin yana ina?" "Yana cikin ɗaki, likitoci sun ce kar a shiga" ai take ya ture Walid, ya nufi ɗakin, ana kar ya shiga, amma ko waiwayowa bai yi ba ya shiga. Wata nurse ya taho ta ce "Ya za ku bari ya shiga, isasshen bacci ake so yayi" Walid ya ce "Dan Allah ki yi haƙuri, yanzu a kan ku hana shi shiga, duk sai ya tayar mana da hankali, ku ƙyale shi dan Allah". Viper kuwa gaban gadon Abbu yaje ya durƙusa, ya ɗora hannunsa a kan cikinsa, ya tabattar da yana numfashi, sai dai still ya kasa yarda, gani yake kamar Abbun ya mutu ne. Ya cigaba da ta tattaɓa duk wasu sassa a jikin Abbun, domin tabattar da yana raye. Caraf ya ji Abbun ya riƙe hannunsa, ya ce "Al'amin" "Na'am, sannu ya jikin naka?" "Na ce ka zo, amma kaƙi zuwa, ko dai haryanzu baka yafe minin bane ba, k yi haƙuri, idan baka yafe mini ba na mutu a haka, na san sai Allah ya tambayeni, tun da kana da hakki a kaina" "Dan Allah ka daina maganar nan, kaima sai ka tafi ka barni? Ba ƙin zuwa nayi ba, aiki aka tura ni wani daji can jos, shiyasa ba wai ƙi nayi ba" Ya kalli Viper ya ce "Aikin menene haka?" "Zan gaya maka amma sai ka warke tukuna in sha Allah" yayi maganar yana shafa saman hannun Abbun. "Matso na rungumeka nima, nayi kewarka sosai" Viper ya gyara zamansa, ya ɗora kansa a ƙirjin Abbu. Ya ɗora hannunsa a kan sumar Viper ya ce "Lallai kana cikin maraici, da jauhar na nan ba zan ganka da wannan sumar ba, Allah ya yi mata rahama" Viper ya yi shiru ya kasa magana. "Al'amin" "Na'am" "Kana ganin idan muka nemi auren yar uwar jauhar za su bamu? Ina son yarinyar ita ma" Viper ya ɗago ya ce "Ka samu ka koma baccinka, zan je na yi salla" Abbu ya ce "To, ka ci abinci ma, ina ga Shahida ta kawo abinci, sauran yaran nawa duk su ci abinci, na ji daɗi yadda duk suka zo suka tsaya tare da ni, Alhaji Bashir ma bai daɗe da tafiya ba, na ji daɗi sosai da sosai." "Tom, amma ka yi shiru" ya fita. Ya tarar daga Nabila sai Walid, da Shahida, liti ma ya zo duk suna zazzaune. Yana fitowa suka fara tambayar sa, ya jikin Abbun. Fuskarsa babu walwala ya ce "Da sauƙi har ma mun yi magana, bari na je na samu wuri na yi sallar la'asar" Nabila na nan zaune, jira take yi, Alhaji mu'azzam take yi wa kwatance, zai zo ya duba Abbu. Bayan mintuna talatin, liti ya amsa waya, ya kalli Nabila ya ce "Viper ya ce ki je" "Ina?" "Wallahi ban sani ba, sai dai ki kira shi" Sai da ta ja lokaci kamar ba zata tashi ba, sai kuma ta tashi, tana tunanin ta ina ma za ta ganshi da zai ce ta je, me ma za ta yi masa. Tana tafe tana waige-waige, kawai ta ganshi a can wani wuri yana amsa waya, ƙarasawa tayi, ta tsaya ya gama wayar, da alama wayar ta shafi aiki ne, yayi ya kammala sannan ya waiwayo ya kalleta. Yanayin kallon da yake yi mata, sai da ta tsorata kamar zai kai mata duka, ya tsuke fuska sosai ya fuskanceta, sannan ya ce "Daga rana mai kamar irin ta yau, ko a waya, ko a zahiri idan ki ka kuma yi mini shouting, ko gaya mini duk maganar da ta zo bakinki, i will mercilessly deal with you, i am not your mate" motsa baki tayi za ta yi magana, amma ta kasa, ya juye mata ya koma mata Vipernsa sak, fuskar nan sam babu annuri. Amma ta sake tattaro jarumtarta ta ce "Ba shouting na yi maka ba, gani nayi idan ba haka nayi maka ba ba zaka zo ba, kuma... "Keep quiet malama, idan ma na zo idan ban zo ba ina ruwanki?" Ta ɗago ta kalleshi, ya sake tsareta da idonsa, dolenta tayi ƙasa da kanta. Ya nuna ta da yatsansa ya ce "This is my last warnin, idan ki ka sake zaki sha mamaki, wuce mu je" zungui-zungui tayi gaba, ya biyo bayanta, zuciyarta kamar ta fashe dan haushi, deep down kuwa a zuciyarsa kewarta yake yi, yanayin yadda tayi masa magana, da yadda ta daina kiransa ne ya ƙara tunzura shi, amma ya ji daɗin ganinta a wurin mahaifinsa da yadda ta nuna damuwarta. Tun daga nesa liti ya hango su, ya san babu arziki faɗa suka yi, ya zo ya zauna Shahida ta zuba masa abinci ta bashi. Liti sai tambayar ƙwaƙwa yakw yi wa Viper, a kan aikin me yaje yi. Suna zazzaune sai ga Alhaji mu'azzam ya zo ya duba baban Al'amin, aka yi sa'a ya ɗan sakar masa fuska, suka yi magana a kan rashin lafiyar Abbu. Har suka keɓe suka yi magana, a kan aikin da yaje yi, tare da shi Viper aka kai ɗan mama can kudancin Najeriya, in da zai karɓi nasa horon na musamman, sai dai bai kai na Al'amin tsauri da takura da kuma daɗewa ba, shi shekara guda kawai zai yi. Suka gama maganar, Kankarofi yayi musu sallama zai tafi, Nabila ta ce "Honorable dan Allah ku ajiyeni a hanya, na samu abin hawa" Kankarofi ya ce "Babu damuwa, ina motarki ne?" "Ta lalace ta zama gwangwani" Ya ce "To Allah ya mayar da sabon alkhairi, amma babu risk a a hawanki public vehicles, ina masu fita da ke?" "Ai na gama aikina, ba wani abu da zai same ni in sha Allah" sai ya lura kamar tana sane, basarwa yayi ya ce "Shikenan muje" yayi musu sallama amma Viper bai sake cewa komai ba. Wami abu mai zafi ya tsayawa Viper, ganin sun jera ita da Alhaji mu'zzam sun yi gaba, amma ya dake ya shanye, yayi shiru ya maze, dan idan ya ce zai tanka ɓatacciya za ayi. Yana Asibiti har dare, Liti ya ce "Boss ka koma gida, mu sai mu kwana da Abbun, ka je ka samu ka huta" Viper ya ce "Ba zan iya tafiya ba, gani nake idan na tafi komai zai iya faruwa, gara na kwana da shi kawai". Walid ya ce "Ba gamu ba, babu abin da zai faru in sha Allah" "I am sorry, ka bar ni kawai" Walid ya ce "To shikenan, na ga dare ya fara yi, bari na raka Shahida gida, sai na dawo" Viper ya ce "To a sauka lafiya" A hanya Shahida take ƙara bawa Walid labarin yadda aka kashe Abba, ya jajanta masa sosai da sosai, saboda abin gwanin ban tausayi, sa'ar da aka yi shi ne an kama yaran da suka kashe shi ɗin. Bayan ya dawo tare suka kwana su uku tare da Abba, yana kan gado, suka yi shimfiɗa a ƙasa, suna hirarrakin su ƙasa-ƙasa dan kar su takura masa, har aka jima kuma su ka yi bacci. Viper kuwa idonsa biyu, ransa a matuƙar ɓace da abin da Nabila ta yi masa, ga kuma kewarta da take ta addabar ruhinsa. Abbu kuwa kallonsu yayi, yadda suka jere su uku a ƙasa a kwance, ya sake jinjina girman ikon Allah. Dukkannin su, kowanne gidansu daban, ba su haɗa wata alaƙa ta jini ba, sai ta rashin jin su, amma sun riƙe juna da tsantsar amana, da ƙauna. Da ya motsa dukkaninsu ƙoƙarin su, su ji meye damuwarsa me za su yi masa, sai ya ji ina ma ace duka nasa ne. Da haka gari ya waye, suka takura Viper ya je gida ya yi wanka sai ya dawo su ma su tafi. Haka aka yi, ya tafi ya je yayi wanka, ya ɗan huta, ya ga message ɗin Nabila "Assalamu alaikum, ya mai jiki? Ba zan samu zuwa yau ba, daga wurin aiki zan je ganin likita, idan kuma na kammala da wuri zan zo in sha Allah, ayi masa sannu" guntun tsaki ya ja, ko arzikin gaisuwa ma bai samu daga gareta ba sai surutu. Lokacin da ya koma, Shahida ta kawo abincin rana, suna zaune a ɗakin Abbu, ya samu har ya tashi zaune ya yi wanka, ya ci abinci. "Ka dawo?" "Eh ya jikin" "Alhamdilillah" Shahida ta gaishe shi ya amsa, liti kamar wanda aka matsa sai cewa yayi "Wai babarku ba ta san an kwantar da Abbu bane, naga tun jiya ba ta zo ba" Shahida ta ce "Ai tun da aka kashe Yaya Abba, ita ma ba ta da lafiya, shiyasa ba ta zo ba" Walid kamar ya zabga wa Liti mari, ko ina ruwansa oho. Viper ya ce "Muhsin yakamata kuma ku je ku huta". "Eh bari mu ci abinci tukuna, ko a gidan ka bar mana abin da zamu ci?" Viper ya harare shi, ya ce "In dawo jiya, yau kuma na hau yi muku girki" "Dama can ma ai mu muke yi, bayar da order kawai ka ke yi, sai ma idan an yi kai ta cewa bai yi daɗi ba" Walid ya ce "Yaushe ma ya fara cin abincin, sai da Nabila ta shigo rayuwarsa, yanzu carryover wanda bai ci ba yake yi". Abbu kallonsu kawai yake yi yana murmushi, yana mamakin yadda suka iya zama da Al'amin, gashi dai ba dolensu ba, amma da shi da halinsa suke iya zaune da shi. Suka ci abincin suka tashi suka fita. Viper ya ce "Shahida ta tashi ta tafi gida, tun da akwai wata mara lafiyar a gida, ba ta yi musu ba, ta tashi ta tafi. Abbu ya kalli Al'amin ya ce "Aminu yaran nan suna matuƙar ƙaunarka, sai suka ƙara shiga raina, Allah ya ƙara muku haɗin kai" "Amin, amma meye ya kashe wa Shahida aure? Ina fatan ba wani rashin kyautawar tayi ba" Abbu ya girgiza kai ya ce "Nima ban san ainihin abin da yake faruwa ba sai yanzu, uwatta ce ta bawa mai kuɗi, da akwai wanda take so, ta ce ita ba shi take so ba, mai kuɗin zata aura". "Abbu kuma ka bari?" "Ya zan yi mata, ta dage tana nuna mini 'yar ta ce, sai kwanan nan Shahidan ta same ni, wai ita ta kai shi kotu, Khul'i za su yi, ya sauwwaƙe mata, na tambayeta dalili ta ƙi faɗa, na kira shi mijin nata ya ce shi ma bai san dalilin ta ba, sai da na ritsa uwarta, sannan take gaya mini wai ba shi da lafiya, tsawon shekaru ukun da suke zaune" guntun tsaki ya ja, ya ce "Da ina nan gaskiya ba zan bari ayi wannan abin ba, yanzu shikenan ta zama bazawara" "To yaya zan yi, makaranta dai nake so ta zo ta koma, gaba ɗaya tausayinta nake ji, halinta ya sha bamban da na uwatta da yar uwatta, ba yadda muka iya da ƙaddara". Viper ya yi shiru bai sake cewa komai ba. Abbu ya sake numfasawa ya ce "Yakamata na gaya maka abin da nake son na gaya maka, kar lokaci ya ƙure mini" Al'amin ya tattara hankalinsa a kan Abbu. "Zuwa yanzu Al'amin babu wani wanda ya san kan kasuwancina sosai, duk wanda na janyo sai yayi ƙoƙarin cutar da ni. Sannan akwai gadonka na mahaifiyarka da kuma ɗan uwanka, sun zama manyan kadarori, kar karɓi abinka ka tallafi rayuwarka, kuma ina son ko bayan babu raina, ka cigaba da jujjuya harkar kasuwancin nan, kar abun da zan bar maka ya ƙare ba tare da ka tsaya da ƙafarka ba" Viper ya gyara zamansa ya ce "Babu in da zaka mutu ka je" Abbu ya yi murmushi ya ce "Faɗa kawai ka ke kaima" Ya rausayar da kai ya ce "Abbu already ina aiki, ni ba zan iya kasuwanci ba" "Aikin me?" "Sojoji nake yi wa aiki, ba zan iya haɗawa ba, ko zan haɗa ma, sai dai wani ya riƙe mini, wasu alfarma nake nema ka yi mini" Cikin sauri Abbu ya ce "Na menene?" "Na farko, ina so ka taimaka ka jagoranci Abdallah, liti ka mayar da shi wurin mahaifinsa, a nema masa afuwa, dan na san nine silar barinsa gida baki daya, ko ba ni bane, na taka muhimmiyar rawa a hakan. Abu na gaba kuma, a yanzu Walid ba shi da kowa sai Allah sai ni, maraya ne, yan uwansa ba sa ta tashi, duk masu ƙaramin ƙarfi ne. Ina roƙonka ka sanya mini shi a harkar kasuwancinka, ka bashi babban gurbi, sannan ka aura masa Shahida" shiru Abbu yayi yana kallon Viper. Ya cigaba da cewa "Na san zaka ga abin wani iri, amma bana zaɓen tumun dare, daga ni har su muna ta ƙoƙarin gyara kura-kuranmu, mu sake sabuwar rayuwa ne. Kuma Walid mutum ne mai amana, ba zai taɓa ci maka amana ba, duk rintsi duk wahala, Walid ba ya cin amana, ni na yarda idan ma ba zaka saka shi a kan naka kasuwancin ba, ka bashi gidana ɗaya, a sayar da sauran kayana, a koya masa harkar kasuwancin katakon, sannan ka aura masa Shahida. Ba kuma dan na cutar da ita ko rayuwarta ba, zan iya yi maka rantsuwa da Allah, ko Walid ba shi da komai, Shahida ba zata wahala ba, ina ƙara tabattar maka da mai amana ne. Shi liti shagon shayinmu yake so, ya ce ko na mutu shi zai gajeta tun da shi ne ya rayata ba ni ba, ya je ya ƙarata da ita, Walid ko duk wani abu da na gada za a ƙarar, dan Allah a bashi ba zan iya biyan bawan Allah nan ba". Abba ya jinjina kai ya ce "Na ga alama, shikenan babu damuwa idan ma ya fi hakan za ayi masa, sai dai ita Shahidan ka yi magana da ita idan ta amince, ka san halin mata kar ayi abu, azo a ji kunya" Viper ya ce "In sha Allah ba za a ji kunya ba, Walid mutum ne mai haƙuri da kawaici, kuma mai amana" "To shikenan, ba zan taɓa maka kayan gadonka ba, amma zan ɗauke shi a kasuwa, zan bashi auren Shahida muddin ta amince, ni ma na shaida ɗawainiyar da yake yi da kai, Allah ya tabattar mana da alkhairi". Likita ne ya shigo yayi musu bayanin jikin Abbu da sauƙi, jininsa ne ya hau sosai, kuma an samu ya sauka, zuwa washegari za a iya sallamarsa. Maƙwabta da abokanan kasuwancin Abbu suna ta zuwa duba Abbu, suna ta so su magantu da ganinsa tare da Viper, ya ƙara girma, da kwarjini sannan akwai alamun ƙarin nutsuwa a tattare da shi. ***** Bunkure ta kasa zaune ta kasa tsaye, saboda rashin sanin abin yi, dan tun bayan da Nabila ta damƙa mata kundin ƙorafe-ƙorafen da zata kai ma'aikatar Shari'a a kanta, ta rasa yadda zata yi. Gashi ma'aikatar shari'ar duk waɗanda ta sani yanzu ba sa nan, an yi musu canjin wurin aiki, tana ta kasa kunne ta ji ta ina za a nemeta. Tsananin damuwa ya sanya ko baccin kirki ba ta iya yi, sai ta sha tayi mankas tukuna. Duk da abokan aikinta, na ta ƙarfafa mata gwiwa, da nuna mata cewa za ta iya fuskantar ƙalubalen da yake gabanta. Ga mutane duk sun dawo daga rakiyar Foundation ɗin ta, kuɗaɗen da suke tallafawa ƙungiyar domin taimakon mutane, duk sun daina saboda sun gano cewa cuta ce. A dalilin Nabila, mutane da yawa suka samu 'yancin yin magana, tare da sanarwa duniya tallafin da aka nema da sunansu, ko aka basu, ana dawowa a karɓa, wasu kuma ma ba a basu. Sosai social media da gidajen rediyo, maganar bunkure ta yamutsa hazo, ko ina zancen ake yi. **** Washegari aka sallami Abbu daga asibiti, suka koma gida. Shahida na ɗakinta, tana kwance tana karatun Alqur'ani, Viper ya ƙwanƙwasa mata ƙofa, ta yi masa iznin shiga, ya shiga ya zauna, ya dube ta ya ce "Kin gama idda ko?" Ta jinjina masa kai, ba tare da ta ɗago ba. "Magana nake son mu yi, shawara ce, ba dole zan yi miki ba, zaki iya cewa a'a idan abin bai yi miki ba" Ta jinjina masa kai. "Na san zaki ji abin wani banbarakwai, amma ba zan yi miki zaɓen tumun dare ba, kuma ba dole zan yi miki ba, ina son Abbu ya haɗa aurenki da Muhsin ne, abokina Walid. Na san zaki yi mamaki, ko ki ji babu daɗi, saboda duba da yanayin mummunar rayuwar da muka yi a baya. Dama kowane mutum tara yake bai cika goma ba, duk wani halin kirki na mutum, sai an tarar da shi da wani hali da ba a so, kuma yanzu muna ta ƙoƙarin gyara ɓarnar da muka yi ne a baya. Ina baki tabbacin Muhsin mutumin kirki ne, kuma zaki ji daɗin zama da shi, ya fi ni nagarta da halacci, da zunzurutun haƙuri. Kema kuma na san mutuniyar kirki ce, a dalilinki ina fatan ya ƙara shiryuwa, amma ina baki tabbacin zaki iya dukan ƙirji a gaba, ki ce kin yi dacen mijin aure. Amma ba dole nake yi miki ba, na tuntuɓe ki ne dai da maganar, kafin nayi masa, idan kuma ba kya son sa babu wani abu shikenan shawara ce". Sai da Shahida ta ji dummm, tabbas Walid ma tsohon ɗan sara suka ne, kuma bata san shi da wata sana'a ba, amma kwana biyun nan da take zuwa asibiti, suka ɗan zauna tare, akwai nutsuwa da dattaku a tattare da shi, kuma karo na farko kenan, da Al'amin ya yi ƙoƙarin yin wani abu a kan rayuwarta, ta san ba zai cutar da ita ba, dan haka ta numfasa ta ce "To yaya duk yadda ka yi dai-dai ne, in dai ka amince, nima na yarda". "A'a kar ki yi mini haka, ki gaya mini abin da yake zuciyarki, ko kuma dai na fara turo shi ya nemi yardar ki da kansa, amma magana ta domin Allah bamu iya soyayya irin wadda ku ke so ba, sai dai ki koya masa, kin san mazaje we are always serious" yayi maganar yana ɗan murmushi. Ita ma murmushin ta yi tana sunkuyar da kai. Nan ya cigaba da koɗa mata nagartar Walid, da ƙoƙarin da ya din ga yi wa rayuwarsa. Za ta iya cewa, ba ta taɓa zama sun yi hirar kirki mai tsawo da yayan nata ba sai yau. Da daddare ya bar gidan, ya tafi can gidan da suke zama, Walid suna ta faɗa da liti, a kan liti yayi musu wanki, ya ce ba zai yi ba, ya saka Viper ya dawo da ɗan mama yayi, tun da ya fi jin maganar sa, dama ɗan mama ne yake yi musu. Viper ya ce "Rabu da shi mai laya, kai ka kusa shiga daga ciki, a din ga haɗa kayan ka masu datti a bayar wanki, ka bar Liti" "Wace zata aure shi, bai iya komai ba sai saka aiki, daga kai har shi?" Viper ya ce "Seriously, Walid Abbu zai baka auren Shahida, abin da ya rage maka kawai ka nemi yardarta" waro ido Walid yayi ya ce "Wane Walid ɗin?" Liti ya yi shewa ya ce "Sai dai kai maigida, Allah ya ja zamaninka ka daɗe ka yi ƙarko irin na dabino, Allah dai ya saka da alkhairi" Walid ya ce "Kai fa mahaukaci ne wasu lokutan, uban waye zai bamu aure a haka? Mai zamani ka daina wannan wasan" Viper ya kwanta ya ce "Ba wasa nake yi ba, da gaske nake, ka nemi soyayyarta kawai, aure zan yi muku, Abbu ma ya san zancen. Kai kuma liti sai dai ka nemo da kanka, tun da na san kai ba gwaninta ake yi maka ba" Walid ya ce "Dan Allah a daina wannan wasan, wai waye ma zai bani wani aure? Dan Allah ka bari ta samu mutumin kirki ta aura" Viper ya tashi zaune, ya dafa kafaɗar Walid ya ce "Kai ma mutumin kirki ne, shiyasa ba zan so wata ta samu ba, alhalin ga ƙanwata, ku daidaita kawai sai da safe" yana gama maganar ya kwanta. Walid ya zauna kamar soko yana rarraba ido, Liti kuwa dariya ya din ga tuntsirawa, saboda har gara Viper ma da Walid, dan shi kamar ma tsoron mata yake ji, shi ko da wasa bai taɓa tare budurwa ba. Liti ya din ga tsokanarsa, yayi masa banza ya kwanta, hango Shahida yake yi, yarinya nutsatsiya yar gayu, wai kuma ta aure shi shi dai abin bai yi masa tsari ba. Washegari za su je duba Abbu da yamma, kamar ya fasa zuwa, saboda gaba ɗaya kunya ce ta kama shi. Kasancewar Viper ya riga su tafiya, ya sanar wa Shahida, su Walid za su zo duba Abbu, dan haka ta shirya, za su yi magana ita da Walid ɗin. Duk abin nan, rahila ba ta san me ake shiryawa ba. Sai bayan la'asar, su Walid suka zo, duk yadda yake ɗan sakin jiki da Abbu su yi hira kasa yayi, ya din ga mutsu-mutsu, kamar ya nutse a ƙasa, liti yana ankare da shi, kamar ya yi dariya. Liti ya ce zai je ya dawo, ya fita ya yi nasa wuri, bayan sun yi wa Abbu sallama, a ƙofar gida Viper ya ce "Na yi mata magana, za ta fito ku yi magana, mu haɗe a jungle" "Dan Allah Viper ka ce da wasa ka ke yi, ni wallahi ban san me zan ce mata ba, wallahi kunya nake ji" "Malam yakamata ka girma, ka yi mata tatsuniya if you like" zai sake magana, suka yi ido huɗu da Shahida, ta fito cikin doguwar rigar abaya maroon. Viper ya yi gaba yana murmushi, Walid ya ɗan diririce. Ta ƙaraso tayi masa sallama ya amsa, ta saci kallonsa, dogo ne shi ma, sai dai bai kai Viper jiki da tsawo ba, kuma yana da haske sosai, sai dai laɓɓansa baƙi ƙirin, idanunsa kuma jajaye, yana da dogon hanci da gemu kaɗan ba mai yawa ba. "Sannu ya jikin Abbu?" "Da sauƙi Alhamdilillah" "Amm na san wataƙila mai zamani ne ya takura miki, idan ba kya so na, ki rabu da shi kawai, Allah ya zaɓa miki miji nagari, rigimarsa ce kawai ta saka ya ce wai zai aura mini ke" yadda duk yake a rikice ne ya sanyata murmushi ta ce "Yaya Muhsin, mu yi addu'a mana, bamu san me Allah ya ɓoye ba, mu nemi zaɓin Allah, in dai nima zaka kula da ni, ka din ga lallaɓa ni kamar yadda ka ke yi masa ai ba wani abu" sunkuyar da kai ya yi yana murmushi, sai dai kamar ya zuba da gudu dan kunya. Bai fi mintuna goma ba, yayi mata sallama. Da ya koma can gidan da suke, kamar wanda ya aikata zunubi, liti ya saka shi a gaba, ko murmushi yayi, sai ya ce tunanin Shahida yake yi, ya hana shi sakat. Da daddare Shahida ta kira Viper, ta tambaye shi ya suka je gida. Maimakon ya bata amsa, sai ya miƙa wa Walid wayar. Tayi masa ya yaje gida, sannan ya ce zai ɗauki lambarta a wurin Viper. Washegari da sassafe, Viper ya shirya ya fice ya bar su, dan yai zai koma wurin likitan ƙwaƙwalwa, kuma yana son ya ga Nabila. *** Ƙarfe tara na safe, Nabila ta fito falon madam Halima, hannunta riƙe da jakarta, da court ɗin ta, kawai ta ga Viper a falo, suna magana da Madam. "Mummy good morning" "Morning sweetheart, kin fito?" "Eh, Good morning" tayi maganar tana kallon in da Viper yake, bai amsa ba, ya ci gaba da magana da Madam. Kitchen ta nufa, kusan mintuna biyar, madam ta tashi ta shiga ɗakinta, Viper ya bi bayan Nabila. Sai da ta tsorata da ganinsa unexpected. Wuri-wuri ta yi da ido tana kallonsa. Ya sauke ajiyar zuciya ya yi ya ce "Abin da ki ka yi mana kina ganin kin kyauta ko? Nayi tafiya mai hatsari, ya na je ya na dawo, bai dame ki ba? Kin yi mini laifi amma ba ki iya bani haƙuri ba, yau zamu koma asibiti you don't even care to call me. And a gabana ki ka bi kankarofi, duk dan ki tura mini takaici". Tayi shiru ta ɗan kalle shi ta ce "Ba faɗa ka ke yi mini ba, komai ka yi ta hantarata" Ya ce "Ke ki ke yin abin da zan hantarekin ai. Akwai muhimman batutuwa da yakamata muyi discussing, kawai kina wani fushi mara dalili. Ana ta matsa mini lamba, za ayi posting ɗina wurin aiki, da zarar na kammala aikin da nake yi a kan Indabo, ina son ayi aurenmu dai-dai lokacin da zan tafi aiki" "Kai da wa?" "Ni da waye a nan wurin?" Yayi maganar yana tsareta da idanunsa. "Allah ya baka madadin matarka da ka rasa, ba zan iya aurenka ba Vi, i fulfill my work on you, amma mu bar wannan maganar Please" Sai da ya nazarceta sannan ya ce "Ƙarya ki ke yi mini da ki ka ce ki na so na kenan?" Ta ɗan ja da baya, saboda tsoron yadda idanunsa suka fara sauyawa ta ce "Ko ma ya ne, kai ka fara discouraging ɗina, a lokacin da ka yi fatali da tayina, ka ce mini ba wannan maganar, bayan jauhar baka kallon kowace mace. Nima kuma na gamsu da hakan ba zan iya auren mijin 'yar uwata ba. Amma Alhamdilillah na cimma burina a kanka, tun da ka dawo yadda take fata kafin ta mutu". "Ba kya so na kenan? Ba zaki aure ni ba?" Ta jinjina masa kai, tana kawar da kanta gefe alamar eh. Juyawa ya yi, ya fara takawa, wayarsa ta fara ringing, ya cirota ya saka a kunnensa ya ce "Na'am" A razane ya ce "What Walid ɗin? How?" Ayshercool 08081012143 100 Cike da gigicewa ya ce "Gani nan, kar ka sanar da kowa" Saboda rikicewa, sai ma ya rasa ina ne hanyar fita, sai daga baya. Nabila ta ce "Vi menene? Meyafaru?" Bai kulata ba, yana ƙoƙarin fita, Madam Halima ta ce "Au nan ka biyota, na zata tafiya ka yi ai" sai dai yanayin fuskarsa ya nuna mata akwai damuwa. "Viper menene? Meyake faruwa ne?" "Walid, gayen nan da muke zuwa da shi, na baro su a gida, ya fita yin refiiling, shi ne bai koma ba, Abdallah ya bi hanya ya tarar da cylinder gas ɗin a gefen hanya, da takalmansa da agogonsa, that means ɗauke shi aka yi" tuni kamanin Viper suka canza, saboda tashin hankali. Yana ƙoƙarin fita, madam ya ce "Wait Viper, tattara hankalinka ka nutsu, tunani al'amarin nan yake buƙata da nutsuwa, ba gaggawa ba. Yanzu na san Joseph ya ƙaraso, zai fita da Nabila, ya kai ka ku je a tabattar da abin da yake faruwa, sannan ka kira Oga ka sanar masa da halin da ake ciki" ya jinjina kai ya wuce cikin hanzari ƙirjinsa na bugawa da sauri. Da sauri Nabila ta ce "Bari na bi shi Mummy, kar ya je yayi wani abun, kin san shi da zuciya da wutar ciki" "Kya ma gama gulmarki ne daughter, Allah ya bayyana shi cikin aminci" ta amsa da Amin. Kafin ta ƙarasa har ya riga ya shiga mota, sai da ta haɗa da sauri, sannan ta ƙarasa ta shiga baya, kasancewar gaban motar ya shiga. Tana shiga ta ji Viper yana waya "Liti kar ka matsa daga wurin, gani nan zuwa, kuma kar ka gaya wa kowa, ka kira wayarsa ne?" "A gida fa ya manta ta a kan window ya fita" "Shikenan gani nan zuwa" "Nabila na ta son tayi masa magana, amma ta san a ƙule yake da ita, dan haka ta ja bakinta ta tsuke" A haka suka isa dai-dai wurin da liti yake, yana ta buge-bugen waya. Yana zuwa ya tarar da Liti a hanyar shiga rukunin kamfanunnukan da a bayan su gidan nasu yake, bai taɓa komai ba, yadda ya tarar da takalman walid, da cylinder gas da agogonsa a yashe. Viper ya yi shiru, yana nazartar wurin, Joseph ma fitowa ya yi, suna dudduba wurin, ya kalli Viper cikin broken English ya ce "Oga, da alama sai da aka yi kokowa da shi kafin a tafi da shi" Su na nan tsaye Viper yana duba wayarsa, sai ga motar Civil defense sun zo wurin, su ka yi wa Liti tambayoyin da yakamata, suka yi investigation a wurin. Su ka yi ta bawa Viper haƙuri, da ƙoƙarin kwantar masa da hankali. Jiki a sanyaye Nabila ta ce "Ka yi haƙuri, in sha Allah yana cikin ƙoshin lafiya, bari na tafi" "Ki shiga mota, mu ajiye ki, zan bi bayan civil defense ɗin nan, na ji me ake ciki" Ta jinjina masa kai, ta shiga mota suka tafi suka ajiyeta a wurin aiki. "Idan kin kammala, ko za ki je wani wurin, ki kira ni kar ki fita, i don't think you are safe". Nabila ta ce "Ok shikenan na gode" Abu kamar wasa, aka shafe kwana biyu, babu Walid babu ɗuriyarsa, hakan ya ƙara ɗaga hankalin Viper fiye da tunani, tun yana ɓoye-ɓoye, har maganar ta fita, sai da ya sanar da Abbu. Duk da ba wata shaƙuwa tsakanin ta da Walid, amma ta san shi da yayanta, kuma yana nuna damuwa da abin da ya shafe su. Sosai hankalinta ya tashi, Abbu kansa da shi ake ta zarya. Alhaji mu'azzam ma sai kwantarwa da Viper hankali yake yi, liti ya fi kowa shiga damuwa, dan kuwa har wata irin muguwar rama yayi, a ƙa'ida shi ne yakamata yaje yayi refiiling ɗin, ya tsaya jan jiki, Walid ya zuciya ya tafi ya yo, tsautsayin ya faɗa masa. Duk in da ake tunanin samun Walid, an duba ba a same shi ba, Liti har wata irin rama yayi. Duk ƙaunar Viper da Abinci, baya gabansa, ba ya iya ci, saboda damuwa da tashin hankali. Gashi yana ta gargaɗin Nabila a kan yawo anyhow, dan ya san tun da aka farmaki Walid, a kowane lokaci za a iya sake kai ma wani na kusa da shi hari. Misalin ƙarfe biyu da rabi na dare, yana zaune ya kasa bacci, yana ta tasbihi, yana fatan Allah ya kuɓutar masa da Walid, wayarsa ta fara ringing. Cikin azama ya ɗaga, ya saka a kunnensa ya yi shiru. "Ban yi mamakin jin idonka biyu ba, saboda sai da na duba, na duba na tabattar da wanda na kama, shi ne na kusa da zuciyarka, da taɓa shi zai tabattar maka da ina sane da kai, ban manta da kai ba". "Ina ka kai Walid, kar ka bari sabgar nan ta juye zuwa wani abu daban, ka fito da shi, duk in da ka kai shi" "Ta daɗe ba ta juye ba, ka manta tare ku ka din ga yi mini aiki a baya, ai ina ganin kamar shi haryanzu ba shi da wani muhimmin tabo, da bangar siyasa tayi masa kamar kai. Ai talaka ba shi da wani amfani, ban da ku yi mana hidima, amma kun dage zaku kai ni ƙasa, zan saki Walid ne, a lokacin da wa'adin zaman Abdul yasar ya ƙare a gidan yari. Sannan zan sake duba abu mai muhimmanci a gareka, na yi masa ɗaurin talala, yana raye amma kamar matacce, kamar yadda ka saka aka ɗaure mini ɗa a ƙasashen waje. Na samu labarin kana aiki a kaina, sai ka ga bayana, gani gaka, ɗan halak ka fasa". Viper ya ce "Wannan shi ne kuskure na biyu mafi muni da ka aikata Indabo. Ni da kai muke harƙalar nan, kuma batun ɗanka, hukunci aka yi masa dai-dai da abin da yayi. Ina mai gargaɗinka da kakkausar murya ka saki Walid, idan ba haka ba zan razana duniyarka da abin da baka taɓa zata ba, awanni arba'in da takwas kawai ka ke da su, kuma ka fara ƙirgawa daga yanzu" yana gama maganar ya kashe wayar, ya dafe kansa, cike da wata irin nadama da danasanin biye wa Indabo ya din ga aikata ɓarna. Wato a duniya idan amfaninka ya ƙare kai ba a bakin komai ka ke ba, meyasa zai ɗauki Walid maimakon ya ɗauke shi, tun da da shi yake yi, ba Walid ba. Da sassafe Viper ya tafi barrack, saboda Nabila, yana tsoron ita ce next target na indabo, tun da tare suke yin komai da ita, sai dai tayi noticing rama da kuma damuwa a tattare da shi. Tana ta shiri, yana falon madam yana jiranta, gani yane da ya kawar da kai, komai na iya samunta. "Vi" ya ji ta kira sunansa. "Ka karya sai mu fita" ya girgiza mata kai bai ce komai ba. Ta fuskanci damuwa na ƙara saka shi miskilanci da rashin magana. Nabila ta sake marairaicewa ta ce "Dan Allah ka ci ko kaɗan ne, duk ka yi wani iri" "In ci Abinci ban san halin da ɗan uwana yake ciki ba? Shi ya ci? Duk a dalilina, shikenan duk wanda ya raɓe ni a haka rayuwarsa za ta ƙare a wahala da tashin hankali, menene laifin Walid ne?" Cikin rauni ta ce "Na sani, na kuma fahimce ka, amma hakan babu abin da zai canza. Addu'a da ci gaba da jajircewa ce kawai za ta kawo mafita, ka yi haƙuri dan Allah Vi ka saka wani abu a cikinka" ya ƙura mata ido na wani ɗan lokaci, kawai ya tashi tsaye ya ce "Idan kin gama ki same ni a mota" sosai tausayin sa ya mamaye mata zuciya. Jiki a sanyaye ba tare da ta samu ta yi breakfast ɗin ba, ta bi bayansa. Da suka kai ta wurin aikin ma, har ta shiga ta ji kamar ana bin ta, ta waiwaya ta ga shi ne ya biyota. Ba ta ce masa komai ba, ta shiga office ɗin ta ya bi bayanta. Kujerar cikin office ɗin ya samu ya zauna, bai kulata ba, ita ma ba ta ce masa komai ba, ta ci gaba da aikinta, gani yake yi yana kawar da kai, wani abun zai sameta ita ma. Har ta gama aikinta na ranar yana zaune, sannan Liti ma ya saka an mayar da shi cikin barrack. Duk yadda ya bi wayar Indabo abu ya gagara, sai taƙi shiga, gashi gani yake yi kamar babu wani ƙoƙari da ake yi a kan neman Walid ɗin. Kwatsam Nabila na shirye-shiryen tafiya, ya sake jarraba wayar Indabo, cikin sa'a ta shiga kuma ya ɗaga, Viper ya miƙe cikin zafin rai ya ce "A karo na ƙarshe, ina Walid yake?" "Babu wata barazana da zaka yi mini Viper, sharuɗɗa zan saka maka, wanda dole sai ka bi su. Na farko ka saka wannan yarinyar ta janye ƙorafin da ta shigar a kan Bunkure a ma'aikatar Shari'a, sannan ka tattaro duk wani bincike da ka yi a kaina, na yinƙurin tona mini asiri, da wannan wayar da ka ke amfani da ita ka bani, sai a saki Walid, idan ba haka ba wannan banzar yarinyar ita ce next target ɗina a kanka, sai na saka an wulaƙanta ta, wulaƙanci mafi muni na tagayyara rayuwarta, fiye da yadda ka ke tunani" Viper ya ɗaga kai ya kalli Nabila da take kallonsa, amma ba ta san me ake cewa ba. Viper ya ce "Saboda abin da nake shiryawa a kanka ne ya sanya ka kashe P.A?" Indabo ya ce "Eh, ban damu da a in da ka samu labarin hakan ba, iyaka na san ba ka da wata cikakkiyar shaida a kan ni ne kashe shi, duk wanda ya ci amanata, sai na kawar da shi. P.A ya ci amanata ya haɗa kai da kai, domin yana ganin ya zame ya bar ni shi ne zai sanya ka ƙyale shi". Viper ya sauke numfashi mai zafi, cike da dana sanin, sanin Indabo a rayuwarsa ya ce "Idan kuma ina da shaidar kisan kan da ka yi wa P.A da hannunka fa?" "Gwargwadon yadda ka ci gaba da zurafafawa, gwargwadon yadda zan ci gaba da hura wutar da ka ke ciki, ba dai kana yi wa kanka iƙirarin ƙarfen cikin wuta ba, idan ba zaka ɗakku da hannu ba, zan ci gaba da iza wutar da ka ke ciki, sai ta kai matakin da zata narka ka" Viper ya datse laɓɓansa na ƙasa, ya fesar da wani zazzafan numfashi, ya ce "A ina zan kawo maka abin da ka buƙata?" "Zan turo maka adireshin wurin, kuma ba kana bayarwa za a sake shi ba, sai na ba wa ƙwararru sun tabattar da ingancin abin da ka bayar, kuma a yau ba gobe ba, yarinyar nan ta janye maganar Bunkure" "Na ji, zan yi abin da ka ce, amma yarjejeniya ɗaya idan ka saɓa, wutar da kake ƙoƙarin narkani da ita, kai zata ƙona" Indabo ya katse kiran. Viper ya kalli Nabila, ta ce "Vi wai lafiya?" "Zamu je ma'aikatar shari'a, ki janye ƙorafin da ki ka shigar a kan Naja'atu Bunkure" A razane Nabila ta ce "Saboda me?" "Saboda haka na ce" yayi maganar a fusace. Nabila ta ce "Akwai dalili dole, ka gaya mini, idan ba haka ba zan iya janyewa ba gaskiya, gaba ɗaya wahalata a kan lamarin matar nan na ɓata lokacina, kawai kuma sai na janye?" "Sai kin janyeta, babu wani bayani da zan yi miki, dolenki ki janye" yayi maganar yana kallon Nabila, yana hasko cikin bala'i da tashin hankalin da zai shiga, idan aka taɓa ta. **** Goye yake da Jaka a bayansa, a dajin Allah shikaɗai, sai waige-waige yake yi. A kan babura da manyan bindigu, wasu mutane suka ɓullo, suka zagaye shi. "Ka ajiye jakar, ka ɗaga hannayenka sama" wani yayi masa umarni. Ya ajiye jakar, ya ɗaga hannayensa, ɗaya ya karɓi jakar, ya zazzage, ya dudduba ya ce "Kayan ne" Wani daga cikinsu ya ce "Za a aika shi ne?" "A'a kai ba a ce ba, jami'i ne, asirinmu zai iya tonuwa, mu ware kawai". Suka ja baburansu, suka yi gaba, suna tafiya aka turo masa saƙo. "Ke je dutsen da yake in da kuke, ka ɗauki gawarsa" kamar mahaukaci, haka Viper ya sake gigicewa, daga in da aka saka shi kai kayan, bai isa in da Walid yake ba, sai bayan awanni uku. Yana zuwa ya lura da ba a lokacin aka yar da shi a wurin ba, kamar ya kwana a wurin, an ɗaure masa hannu da ƙafafuwa, an tura masa tsumma a baki, an ɗaure wuyansa da wayar cable, ga jikinsa ko ina a farfashe saboda duka. Fuskarsa ta kumbura suntum, duk jini, ƙanan ƙwari sai bin sa suke yi. Kamar yaro ƙarami, Viper ya fashe da kuka yana kwance Walid, ya kwance wayar da take wuyansa, ya ɗaga shi yana kuka, yana kiran sunansa. Ya ƙanƙame shi a jikinsa, kawai ya ji zuciyarsa na bugawa, a hankali. Zumbur ya miƙe, yana ambaton Allah, ya goya shi a bayansa, gani yayi idan ya tsaya buge-bugen waya, zuciyarsa zata daina bugawa, haka ya kwashi tafiya, har rukunin kamfanunnukan nan, ya ce su taimaka masa su kai Walid Asibiti. Kai tsaye barrack ya tafi da shi, ya kai shi asibitin cikin bariki, babu wani jinkiri aka rufu a kansa, yana da rai bai mutu ba, sai dai babu tabbacin ya tashi. Duk da Nabila tana cike da ɓacin rai da damuwar sakata janye ƙorafi da yayi, ba tare da ya yi mata bayanin komai ba, amma tana ganin saƙonsa na yana Asibitin cikin barrack tare da Walid, ta tashi tana tsuma, ta saka hijjabi ta fita. Yanayin da ta ganshi ne ya karya mata gwiwa. Ta ce "Vi ya ake ciki?" "Yana ciki sai dai babu ya rayu" yayi maganar yana zubar da hawaye. "Kayi haƙuri vi, ka kwantar da hankalinka, in sha Allah Walid zai tashi da ikon Allah" Sai ita ta kira su Alhaji mu'azzam, da Liti ta sanar musu an ga Walid. Babu jimawa wurin ya ɗinke da jama'a. Hatta Abbu yana wurin, Shahida ma kasa zama tayi, sai da ta biyo Abbun. Abbu sai shi ya kama hannun liti, yana ta rarrashin sa, gaba ɗaya ya firgice, an tuɓe Walid daga shi sai gajeren wando, duk jikinsa shaidar duka, aka yi dressing ɗin raunukan jikinsa, aka ɗebi jininsa ana ta gwaje-gwaje. Duk wani abu da za a buƙata wurin bincike, sai da suka ɗauka, kafin a taɓa shi. Ɗaya daga cikin likitocin ya fito, ya ce "Ku kwantar da hankulanku, Alhamdilillah. He's responding to treatment. Vitals ɗin sun dawo normal, in sha Allah muna saka ran ya farka a kowane lokaci. Idan ya farka zamu tura shi sauran gwaje-gwaje. Sai a lokacin suka ɗan samu nutsuwa. Cikin dare aka kira Viper wurin ogansa, Ya sha faɗa a kan abin da ya yi ba tare da ya sanar musu ba. Shi dai yayi shiru, dan a halin da yake ciki, babu umarnin wanda zai iya tsayawa saurara, ya sha faɗa duk da yayi bayanin abin da ya faru a yanzu. Ya numfasa ya ce "Jami'anmu sun tafi, za su dawo da wayar, duk wanda aka kama da wayar ɓatar da shi zamu yi, cin amanar ƙasa da ƙoƙarin tonon asiri ne, duk wanda aka kama da wayar ba jami'inmu ba" Viper dai yayi shiru, domin an ce ya saurari punishment ɗin da za ayi masa. **** Sai da Walid ya kwana a Asibiti, ya wayi gari, sannan ya motsa ya farka. Liti ne ya ga ya motsa hannunsa, ya tashi da sauri, ya nufe shi yana zazzare ido yana kiran sunansa. Walid ya buɗe ido ya kalli Liti, ya yinƙura zai tashi Liti ya ce "Kai kar ka tashi, a asibiti kake" Ya ɗaga kai yana kallon ɗakin, Viper ya ƙaraso, yana cewa "Mai laya, kalleni ka gane ni?" Murmushi ya yi ya ce "Na kiyayi mai zamani" Viper ya rasa me ma zai yi dan farinciki, ya zuba masa ido, yana haɗiye ƙwalla. "Na kasa tashi ku ɗaga ni" Viper ya sako hannu ya ɗago Walid, sai da ya yi ƙara saboda ji yayi kamar su na kakkarya shi. Liti ya ce "Wai dan Allah meyafaru, suwaye suka ɗauke ka?" "Jama'ar Indabo ne, wai sai na gaya musu abin da Viper yake shiryawa a kansa. Na ce ban sani ba, na daku tun da suka ɗauke ni, a ɗaure nake, sai ranar da suka shaƙe mini wuya da cable na zata mutuwa ma nayi wallahi" Viper ya ce "Muhsin, ka yi haƙuri, duk ni ne sila ka yafe mini dan Allah" Walid ya ce "A'a rashin jinmu ne dai sila" Likitoci sun yi mamakin ganin Walid a zaune yana ta magana. Sai dai aka yi masa wanka, aka saka masa kaya, ya ci abinci, aka je aka yi masa hoto, aka tarar da karaya a hannunsa na dama. Da yamma Viper yaje har gida, yake gaya wa Abbu yanayin jikin Walid, suka yi ta murna, Shahida tana son ta ce masa tana son sake zuwa duba Walid, amma ta kasa. Babban abin da ya tsaye mata, bai wuce jin yadda yake bawa Abbu labari cewa Walid ba shi da uwa ba shi da uba, ba wa ba ƙani, shikaɗai yake gararambarsa, dangin iyayensa ba masu zuciya bane ba, duk ba su da ƙarfi, amma babu wanda ya damu da shi a cikin su. Lokacin da Viper ya yi wa Shahida tayin auren Walid, ita dai ba ta ji tana son shi ko akasin haka ba, amma abin da Viper yake gaya wa Abbu, na cewar maraya ne gaba da baya, sai ta ji wani irin matsanancin tausayinsa, ya cika mata zuciya. Ta ji zata iya kowace irin sadaukarwa, domin rayuwa da shi. Sai dai ta sha mamaki jin cewa wai har ya farfaɗo ya tashi yayi magana, dan lokacin da ta je, baya cikin hayyacinsa. A cikin daren ranar, aka yi wa Walid ɗori a hannu, wajen ƙarfe biyu aka fito da shi, liti ya ce Walid sai ya matsa masa saman gadonsa sun yi squating, tun da shi ne zai kwana da shi, kar yaje yana bacci a zo a sake sace shi bai sani ba. Abin ka da an kwana biyu babu bacci, yana hawa gadon, sai bacci, Walid kuwa zugi ya hana shi bacci, tun bayan da alluran da aka yi masa suka sake shi. Da Viper ya zo ya tarar da su, fizgo liti ya so yi daga kan gadon, amma Walid ya hana shi. Duk wata sangarta da rashin mutunci, idan suna tare liti ya iya ta, amma idan aka fita fagen rashin mutunci na 'yan daba, babu wasa. Viper ya ce "Shahida na gaisheka, ta ce ayi maka sannu" Kawai yayi murmushi yana kawar da kansa gefe. "Au ba zaka ce kana amsawa ba? Aishikenan. Ni dai ina ta sake yi wa Allah godiya, da Allah sa ka farfaɗo, da ka mutu ba zan yafe wa kaina ba, kuma da tarayyar mu, ba ta da wani amfani, Allah ya ƙara tsare mini ku, ya baka lafiya". Walid ya ce "Tarayyar mu tayi mini rana ni, Viper nifa abin da ka yi mini, ban ga wani abu da zai sameka na ja da baya na barka, babu shi. Ka yi mini da aljihunka da jikinka, da lafiyarka babu wanda baka wahalata mini.... "Ka daina wannan maganganun, bau ne past ya riga ya wuce, kuma ni mahaifiyarka tawa ce, a haka na ɗauki abin" Yayi murmushi ya ce "Mai zamani, wanda zai tsaya maka, a lokacin da baka da komai, ka ke neman taimako, ba tare da tsangwama ko tunanin samun wani abu daga gareka ba, baka da babban masoyin da ya wuce shi, shiyasa da kai da mai gida dodo, ba zan gushe ba ina yi muku fatan alkhairi, da roƙa mana gafarar Allah" Viper ya ce "Nima hakan take ai, a duniya yanzu bani da tamkarku, da kai da wannan garujen" yayi maganar yana nuna liti. Walid ya kalli liti yana dariya. "Ya fi ni shiga tashin hankalin rashin ganinka, baya bacci, baya iya cin abinci wai ina zai saka kansa, babu kai ɗan mama" dariya suka yi tare, liti kuwa bai san suna yi ba. **** Ƙaton ɗaki ne babba sosai, ɗauke da computers, da wasu na'urori, Viper yana zaune a kan computer da shi da wasu a cikin wurin. Wani video ya kunna, aka saita a jikin majigi, Videon babu murya, amma Imdabo ne a ciki, yayi wasu maganganu, P.A yana ja da baya, kawak ya harbe shi sau uku da bindiga. Viper, mutumin nan yaƙarsa sai da techniques, ba za su taɓa bari a hukunta shi a cikin ƙasar nan ba, ya aka yi ka samu Videon?. "Eh kamar yadda na gaya maka da farko ne, P.A ɗin sa ne ya samo mini wasu informations ɗin a kansa, saboda a zaman kotu ya ɗauka za a ambaci sunansa, yayi hakan da a wanke shi. Lokacin da Indabo ya buƙaci ganinsa, na bashi cameran, na ce ya saka a gaban rigarsa, zan din ga ganin komai, ni kaina ban yi zaton zai kashe shi ba". Mutumin ya dafa kafaɗar Viper ya ce "Ka kwantar da hankalinka, na san yadda ka ke ji a zuciyarka a kan mutumin nan, kuma na san legally ba zasu hukunta shi ba, tun da yanzu ayi shiru da maganar tuhumar da ake yi masa. But you have my support hundred person, either legally or illegally sai mun ɗauki mataki a kansa. Saboda ba shi da amfani a cikin al'umma ko kaɗan, da kunya ace irin wannan ne suke mulkar al'umma, amma ba wani abu in sha Allah" Cikin damuwa Viper ya ce "Sir na baku recording na wayar da muka yi da shi, yarinyar da zan aura, tana cikin hatsari sosai da sosai, ban san me zai iya yi mata ba, ba zan iya jurewa ba idan ya taɓa ta, ga aikinta da ta sha wahala a kai ya salwanta" "Bai salwanta ba Viper, kuma ina baka tabbacin babu abin da zai sameta, babu kuma abin da zai samu wani naka, kar ka damu" Viper ya jinjina kai yana jin ƙwarin gwiwa. Asibiti ya koma wurin Walid, ya tarar da Shahida, ta yayyanka masa ayaba a kan plate, ta ajiye masa yana ɗauka da hannun hagu yana ci, yana ganin Viper ya zabura, kamar wanda yake aikata rashin gaskiya, sai da Viper ya so yayi dariya, amma ya maze. A haka Nabila ta zo ta tarar da su, tayi masa sannu, Walid yayi ta yi mata godiyar suna ɗawainiya da shi. Nabila ta ce "Vi ai su suka sha ɗawainiya, dan Allah tun da ka farfaɗo ka saka shi ya ci abinci Please, haryanzu baya mayar da hankali, duk ya rame. Ya fi yi mini kyau lokacin da kumarinsa" Walid ya ce "Vi an ce ka din ga cin abinci ka rame" "Zan zageka da kai da Vi ɗin" "Allah ya baka haƙuri, an hanamu faɗar master, Vi ɗin ma an hanamu, to ai shikenan" Nabila ta rausayar da kai ta je bayan Viper ta yi ƙasa da murya ta ce "Zamu je ganin likita kar mu makara fa" ɗagowa yayi ya kalleta, kamar ba zai tashi ba, sai kuma ya tashi ya nufi hanyar fita. Fitarsu ke da wuya ya tsaya cak, ya waiwayo ya kalleta ya ce "Kar ki sake ƙoƙarin yi mini yawo da hankali, ko kuma nuna kin damu da ni, bana son yaudara" yayi maganar yana nunata da yatsansa. "I don't fake it, kai baka san halin da ka saka ni ba, lokacin da na nuna maka so saboda Allah. Na ji da farko i fake it, daga baya kuma da gaske na ƙaunace ka Vi, yakamata ƙwaƙwalwarka ta tunatar da kai, abubuwan da ka yi mini, kuma ka gaya mini. A gabanka abokinka har ce mini yayi bani da class, ina yawo a cikin maza, duk dan ina sonka, ina fatan daga kaina, zaka din ga kiyaye abin da zaka gaya wa mace, mata bama mantuwa. Duk motsin da nayi ban taɓa burgeka ba, kullum cikin kyarata ka ke yi, amma haryanzu ina yi maka kallon abu mai muhimmanci a gareni, mussaman kulawar da Jauhar ta samu a wurinka, ka yi mini afuwa Vi, bana fatan ƙuntata zuciyarka". Cikin tsananin dakiya da jarumta, ya jinjina kai, ya ce "Na fahimta" Duk yadda ya so cire Nabila daga zuciyarsa abu ya gagara, sai a lokutan nan, da ta fara yi masa wulaƙanci ya ga ashe ya shaƙu da ita, shaƙuwa ba ta wasa ba. Cikin ikon Allah Walid ya samu kulawa sosai da sosai, gashi ba shi da ƙan jiki, nan da nan jikinsa ya fara warkewa, sai dai ya kan manta da ba shi da lafiya, idan yana riƙe da wayarsa, Shahida tana turo masa saƙonnin, babban abin da ya ƙara yi wa Shahida daɗi, ita kanta kunyarta Walid yake ji, balle yayi kule-kulen mata, saɓanin mijin da ta rabu da shi, saboda yana da kuɗi, yan mata kowa ma kulawa yake yi, kishi kamar ya kasheta, gashi ba abin da yake iya amfana mata. *** Sallamar da ake ta dokawa a tsakar gida ne, ya sanya dattijon mutumin, sauke farin tabarau ɗin fuskarsa ya ce "Waye ne?" Ya bankaɗo cikin ɗakin ya ce "Nine, ko har an manta da ni ne, nake ta sallama aka yi shiru?" Dattijon ya ce "Ina fa, waye ya isa ya manta da sarkin gida? Maraba lale da Abdallah" Liti ya ƙarasa ya na faɗin "Likkafa ta ci gaba, gida ya sha gyara" "Yau kai ne a gidan ka tuna da mu kenan?" "Ai kullum kuna raina, na san ina zuwa dattijuwarka za ta tayar mini da hankali, ta saka ka kore ni" "Hmm sannu, na samu labarin ɗaya uban naka yayi free, kotu ta wanke shi ko?" "Aiba shikaɗai ta wanke ba, har mu, ai bamu da wata nutsuwa idan yana cikin damuwa. Ban ga tsohuwar nan ba, ko ta rasu" "A'a ni uwata ba ta mutu ba, tana nan ƙalau, sun fita da gyatumarka" Liti ya ce "Lallai ta sha miya, amm Alhaji, dama na zo baƙi ne, wata bazawara ce take so na, shi ne ta turo iyayenta, suka zo nema mata aurena wurinka, tana fatan zaka bata ni" "Ikon Allah, ita bazawarar" "Eh, amma dan Allah kar ka yarfa ni, ko ka tona mini asiri ka ce wai ba na ji, abu ne da aka yi shi ya wuce, yanzu na shiryu na daina, dan Allah kar ka ce musu wai bana ji, kaga sirikaina ne" Alhaji ya yi dariya, ko bayan shekara dubu, Abdallah ba zai canza hali ba,duk da Ya lalace yana son abin sa, amma gwaggo mahaifiyarsa ke nema tayi masa baki, saboda soyayyar da yake yi masa, kuma hakan yana da alaƙa da tsanar da ta yi wa babar litin  ya ce "To Baba, ba zan yarfaka ba" Liti ya fita waje, yayi musu iso, Abbu ne tare da Baba, mahaifin jauhar, da kuma Viper. Alhaji ganin Liti da manyan mutane, ya tashi ya karɓe su cikin girmamawa. Bai fi sau biyu ya taɓa ganin Viper, yanzu da kyar ya gane shi, saboda lokacin da ya san shi yana da ƙuruciya sosai. Nan Abbu ya gabatar masa da kansu, tare da gaya musu abin da ya kawo su, a kan yayi haƙuri, ya yafewa Liti, tun da yanzu duk sun watsar da shirirtar da suka yi a baya, dama har da ƙuruciya. Nan Alhaji yake sanar da su, yadda ya kai liti ƙasar waje karatu, amma ya dawo an koro shi, sai ma shaye-shaye da ya koyo, ga rashin kunya da yake yi wa kakarsa, wanda hakan ya ƙara tunzura shi a kan litin. Viper ya ce "In sha Allah Alhaji, Abdallah ya shiryu ba zai sake ba, dan Allah ayi mana afuwa, ayi haƙuri" Alhaji ya ce "Dama baku muke ƙi ba, halayenku ne ba ma so marasa kyau, Ubangiji Allah ya ƙara rufa mana asiri" Nan kuma hira ta ɓarke a tsakanin su Abbu, tare da tattauna manyan matsalolin da ya jefa yaran nasu ga halaka. Bayan sun gama da gidan su liti, suna tafe, tausayin Walid ya mamaye zuciyar Viper, su duk sun daidaita da iyayensu, shikuwa ba shi da kowa, sai Allah sai barbaɗaɗɗun danginsa marsa amfani. Yayi Addu'ar Allah ya sa Shahida ta rayu da abokin nasa cikin aminci da mutuntawa, mussaman da ya ga ya fara sakewa da Shahidan. Maganar Baba ce ta dawo da shi hayyacinsa da ya ce "In sha Allah, gobe zan je gidan Major, mu yi wadda za mu yi, ya bani 'ya ta, na ƙarasa riƙonta na aurar da ita, na fuskanci bai san zuru ba". Ayshercool 08081012143 101 Abbu ya ce "A'a Alhaji Bashir, abi komai a hankali, zamu je mu same shi sai a tattauna". "Alhaji Ibrahim, na san na yi wa maitama laifi, amma yadda yayi reacting ban ji daɗin hakan ba. Gaba ɗaya ya tsaya mu fuskanci juna yaƙi, ya mayar da ni kamar maƙiyinsa nima fa a ƙa'ida yayi mini ba dai-dai ba". Sai a lokacin Viper ya ce "Baba dan Allah ka yi haƙuri ku sasanta, wannan rashin jituwar taku, yana taɓa Nabila sosai da sosai. Kuma haryanzu tana cikin barrack a zaune, ta rasa yadda ma zata yi dan Allah ku yi haƙuri ku sasanta". Baba ya ce "Ba ƙi na yi ba Aminullahi,  na bashi duk wata dama, a matsayin sa na wanda yake uba a gareta, kuma ya raineta, idan ya gaji ni ya bani abata, nima na rayu da ita ko yaya" Viper ya ce "Haka ne, kana da gaskiya. Amma ka yi haƙuri dai, a bi komai a sannu, aje a same shi, ayi masa bayani, na san zai fahimta in sha Allah" haka Viper ya ci gaba da rarrashin sa. Alhaji kuwa hira suka ɗora da Liti, kamar ba barin gida yayi, kusan shekara guda bai ganshi ba. Ya din ga bashi labarin gwagwarmayar da suka sha, da halacci da kirkin matar Viper, tare da ba shi labarin yadda Nabila ta shigo rayuwarsu, ashe 'yar uwar marigayiyya ce. Sallama aka yi a tsakar gida, Alhaji ya amsa, Liti kuwa ya tsuke fuska. Sai da mahaifiyarsa tayi turus da ta ganshi, ta ce "Abdallah yau kuma kai ne a gidan" "Saboda ba sunan babanki bane ba, kuma ba sunan mijinki bane ba, shiyasa ki ke faɗar sunan yadda ki ka ga dama kamar ke ki ka raɗa masa, to sunan mijinki usmanu ki ka faɗa" tsohuwar da suke tare ta yi maganar a hasale. Ta mayar da idonta kan liti ta ce "Sannu ɗan nema, kai kuma sai yau Allah ya dawo da kai, shanshani mai ƙafar gantali" "An saka mini sunan kirki, saboda wani sunan mijinki, kin ɓata mini suna wani liti. Kuma nan fa ke ki ka saka aka koreni, ba dole na tafi ba, ni wallahi na zata ma kin mutu" "Salamatu ce zata mutu ba ni ba, babarka ba" "Kowa ma dai sai ya mutun nan, duk ƙulafucin mutum da duniyar kuwa" Alhaji ya yi gyaran murya ya ce "Baba gwaggo ce fa, mahaifiyata ce" liti yayi shiru yana hararta. Mahifiyrsa kuwa kallonsa take yi, ta zata tafiyar da yayi, zai sake lalacewa ne, dan abin yana damunta, amma sai ta ga kamar ya ɗan nutsu, babu askin banza, gashi normal shiga yayi, kuma babu alamar buguwa a tattare da shi. Har yamma yan tare da mahaifinsa, saboda ya fi shaƙuwa da shi, yan uwansa duk mata ne suna gidan aure, shi ne kawai namiji. Da yamma aka gama abincin dare, aka zuba masa, ya saka fulasan a leda ya ce tafiya zai yi. Alhaji ya ce "Ina kuma zaka je?" "Can in da nake mana Aljaji" "Au sake barin gidan zaka yi?" Liti ya ce "A'a, dama zuwa nayi ai na gani, idan zaku haƙura ku yafe mini to, idan kuma naga za a sake tozarta ni, idan na cika wandona da iska nayi gaba, in tafi ikko. Amma Alhamdilillah na ji daɗi da naga ba a hantare ni an koreni ba, wurin yan uwana zan koma, Walid ba shi da lafiya yana Asibiti, ni nake kwana da shi, amma zan dawo ai. Na gode sosai da ku ka yafe mini" "Dama ba tsanarka muka yi ba babana, halayen da ka ke yi ne bama so, amm Alhamdilillah daga kai har uban ɗakin naka, naga nutsuwa a tattare da ku, Allah ya ƙara shirya mana ku" "Amin ya haiyyu ya ƙaiyyum, na gode sosai da sosai Alhaji" Alhaji ya ce "Jeka Allah ya bayar da sa'a" ya amsa da Amin. Gwaggo ta fara masifa ta ce "Au barinsa zaka yi ya tafi? Kana kallonsa?" "Gwaggo ki yi haƙuri dan Allah, ba kowane lokaci ƙarfi da fushi yake amfani a wurin tarbiyya ba, wasu lokutan rarrashi da addu'a suke buƙata. Yanzu barin gidan da yayi, ba wai hakan ne ya saka ya ɗan nutsu ba, addu'a ce kawai, kina ji da tasirin wata yarinya a rayuwar abokinsu" "To shi ma ayi masa auren mana, tun da ya fara tsufa yana shashanci" Ficewa Liti yayi, dan idan ya biye mata, lokuta da dama a baya lokacin yana kan ganiyar shaye-shaye, ya sha yinƙurin ɗura mata ashariya, ko kuma ya sureta ya buga da ƙasa, saboda a cewarsa tana yi masa shishishigi da munafunci. ***** Saƙo ne ya riski Naja'atu Bunkure, a kan cewar ma'aikatar Shari'a ta soke lasisinta, har sai an kammala bincike a kanta. Hankalinta yayi mummunan tashi, ta kira Indabo a waya cikin tashin hankali, yana ɗagawa ya ce "Ya kuma aka yi?" "An soke lasisina daga ma'aikatar shari'a, wai sai an kammala bincike a kaina, dama ba ta janye ɗin ba?" "Kuma dai? Ta janye ƙarar fa, sai da na tabattar da hakan, kuma yanzu nima nake samun labarin wannan shegen yaron da na saka a kashe, dan ya ƙara zama jan kunne ga Vipern, bai mutu ba, wai yana raye a asibiti" "To ni ina ruwana, licensed ɗi na fa aka yi siezing, wane irin abu ne wannan, duk wahalar da na sha kafin na zo wannan gaɓar, sai da na kai ƙololuwa sannan zan yi faɗuwar baƙar tasa, wannan mummunan ƙarshen, wallahi ba zai yiwu ba" "Ki yi haƙuri ki daidaita nutsuwar ki, zan san abin yi, ki yi haƙuri ai hakan ba zai yiwu ba sam" kashe wayar tayi, tana jin yadda kanta yayi mata wani irin mugun nauyi, ta ma rasa me za ta yi ko ta ce gaba ɗaya. *** Walid jiki yayi kyau sosai, Viper yana gefensa yana yi masa magana, amma hankalinsa yana kan wayarsa da yake dannawa da hannu ɗaya. "Ɗan marayan zakina, ya jiki, ina son na zo na ƙara dubaka, amma ina jin kunyar yaya, kuma ga mama babu lafiya ita ma" "Kar ki damu, ina samun saƙon gaisuwarki ai, jiki Alhamdilillah da sauƙi" "Allah ya ƙara tsare mini kai" "Amin ke ma haka" "Amma Yaya ya gaya maka na taɓa aure, har shekara uku?" Walid yayi mata reply da"Har ɗaurin aurenki mun je ni da Walid a madadinsa a lokacin yana tsare a gidan yari" "Lallai kun cika abokan amana, ina son abotarku. Amma kana ganin babu ƙwara a ciki, kaga kai ba ka taɓa aure ba, ni kuma na taɓa" Walid ya ce "Ko kaɗan, Viper ba zai haɗani da abin da ya san akwai cutuwa ba, kuma ni ba wannan nake dubawa ba, nima kin san irin rayuwar da muka yi a baya, kuma ni ba wani mai ƙarfi bane ba, buga-buga ce dai muke yin ta, amma kin ga ke kuma 'yar gayu ce, matar manya ce, ina fatan hakan ba zai zama da shiga hakkinki ba" Voice message ta yi masa, ya rage volume yana saurara ta ce "Babu wannan maganar, ni kawai sonake nima ka so ni kamar yadda ka ke son Yaya Al'amin, ka ji my, Allah ya sa kai nawa ne nikaɗai, kuma ka daina ce mini Shahida gaskiya, sunan soyayya zaka samo mini nima" ta ƙarasa maganar tana dariya, dan ta san ƙarshenta, sauka zai yi daga online ɗin. Aikuwa haka yi, ya rufe data yana murmushi, sai suka yi ido huɗu da Viper, da ya gaji da magana ya zuba masa ido, sai yayi sauri ya ajiye wayar yana ɓoyeta kamar yayi rashin gaskiya. Viper ya ce "Wai me ka ke yi a cikin wayar ne?" "Tilawa" yayi maganar yana mazewa. "A'a karatun kalaman da tayi maka kake yi wa tilawa kenan, ai fa Walid an fara soyayya babu sarki sai Allah, muna zaman zamanmu Viper ka saita masa hanya, yake ta zaƙewa" Viper ya ce "Ai naga alama, me take gaya maka ne har haka?" Liti yayi farat ya ce "Wai ɗan marayan zaki, wani gursumemen gardi, kwana yake yana murmushi" Viper ya yi murmushi ya ce "Na ji daɗin hakan sosai, ɗan uwana na cikin farinciki, Allah ya tabattar mana da alkhairi. Kai kuma goga wa zaka samo mana ne mu aura maka?" Liti ya ce "Mhmm, wani zance mara amfani tsohuwar nan ta gidanmu take yi, da na lalace cewa tayi a koreni, Alhajinmu yana sangarta ni, saboda ba ta son uwata. Amma akwai jikarta da take son uwatta, ta gama lalacewa yarinyar nan na girmeta, amma saboda tsabar yawo da gantalin bin maza, duk ta fara tsufa wai a haɗamu aure" Viper ya ce "A'uzubilalimatillahi" Walid ya ce "To meye a ciki, ku rufa wa juna asiri shikenan" "Wa za a rufa wa asirin? Wallahi da budurcina ba zan auri lalattaciya ba, ta gama bayar da free services a kwararo ba, Allah ya kiyaye" "Walid ya ce "A gidan uwar wa ka ke da wani budurci, mace ne kai? Kai ma fa a lalacen nan kake, shaida ɗaya zan yi maka bama kula 'yar kowa" Ya ce "Yauwwa to barka, a bar ni da ɓalla ƙarafa da caji, amma banda shashanci, dama aure ta taɓa yi da sauƙi, amma ta gama gantali wai a bani, kai tsohuwar nan ba ta ƙaunata" Viper sai da yayi dariya, jin yadda liti yake ta ɓaro zance. Tashi ya yi ya fita, yana son ganin Nabila sosai da sosai, amma ya fara tsorata da abubuwan da take yi masa, ya kasa gane da gaske take yi ba ta son shi, ko kuwa dai kawai rigima ce irin ta ta. Wayarta ya kira, sai dai sai da ya fara harzuƙa sannan ta ɗaga, murya ƙasa-ƙasa ta yi masa sallama. "Kina ina?" "Na je gidanmu ne" "Meyasa ki ka fita? Ban gaya miki kina cikin barazanar rashin tsaro ba?" A hankali ta ce "Joseph ne fa ya kai ni" tayi maganar kamar a shagwaɓe. "Meyafaru muryarki tayi ƙasa?" Nabila ta ce "Bana jin daɗi ne, bani da lafiya" "Meyafaru?" Ya faɗa kamar an yi masa dole. "Ka san an yi ƙura ne jiya, ina ta fama da tari, ban yi bacci ba sosai, sai kuma na tashi da ciwon kai" Ya ɗan lumshe idanunsa ya ce "Asibiti fa?" "Na sha magani a gida, zan kai rahama awo gobe in Allah ya kaimu zan ga likita daga nan" Ya ce "Ok take care, idan da wani abu let me know" Ta ce "Ok na gode sosai, a gaida Oga walid" Ta ajiye wayar tana jin wani iri a jikinta, tunani take yi, ko ya daina sonta ne, ya ajiye maganarta a gefe kamar yadda ta nema?. Shi ma sauke wayar ya yi,  yana jin yayi kewar rigima da shagwaɓarta, kenan da gaske dai ba ta son sa kenan? Bai taɓa tunanin idan yayi mata maganar aurensu, za ta ce ba zata aure shi ba. **** Ramma ciki ya tsufa sosai, kullum cikin lissafi take, yaushe Abdul zai fito, gashi sati huɗu ake bata a wurin awo, wani abun tana ji tana gani, tana so, amma babu yadda ta iya, sai dai ta haƙura tayi shiru. Saboda tana tsoron tayi wani abun mama ta hantareta, dan sam ba ta ƙaunar cikin nan. Ramma ta san da Abdul ba a tsare yake ba, da zata ga gata da kulawa, amma tana matuƙar jin daɗin yadda Nabila take nuna mata kulawa da damuwa da ita da sumayya. Yau bayan ta kai ta awo, suka biya aka yi sayyayar kayan haihuwa. Daga nan ta kaita wurin Abdul, yau ma kamar kar su rabu, sauransa wata ɗaya ne ya fito daga prison, bakin ramma har kunne saboda murna. Washegari da yamma, Alhaji mu'azzam ya zo gidan, mama ta karɓe shi, kamar yadda ta saba har take tambayarsa yaushe za su koma ƙauye, sun zo sun zaune masa a gida. Ya ce "Haba Hajiya, ai kin girmi rayuwar ƙauye yanzu, ko dan asirin rahama, ba zaku koma ƙauye ba, kema kuma ina fatan Allah ya baki mijin aure, kema ki yi aurenki a nan birni ki huta". Maman ramma ta ce "Ashha, ga 'ya har da tsohon ciki nayi aure, ai aure kuma yanzu sai dai naga ana yi wanda nayi Allah ya sanya albarka" Alhaji mu'azzam ya ce "Saboda me, shekarunki nawa ne?" "Na kusa arba'in idan ma ban yi ba, tun ina shekara sha uku aka yi mini aure" "Kuma ki ce kin wuce aure, a'a ai aure garkuwa ne" Yayi waya aka shigo masa da wata shirgegiyar akwati, ya saka aka kirawo masa ramma. Ya ce "Sannu rahama, kin kusa shiga watan haihuwa ko?" Ta bashi amsa tana sunkuyar da kai ƙasa. "Babu wata matsala dai ko? Nabila na kai ki awo, naga an ware ni a gefe ni, ke da ita kuke abinku" ta sunkuyar da kai tana murmushi. "To Allah ya raba lafiya, ga kaya nan, naki da na jariri unisex ne kayan babyn, Allah ya raba lafiya" Maman ramma ta ce "Haba Alhaji, ɗawainiyar tayi yawa, jiya fa sun sayo kaya da Nabila" "Wannan mijinta ne ya bayar da kuɗin, wannan kuma ni a matsayinta na 'ya ta na saya mata. Kar ki manta a gidana fa koma menene ya sameta, dan haka ko me zan yi wa rahama, ba zan goge muku abin da aka yi muku ba, dan haka ba wani abu bane ba, Allah ya raba su lafiya" Mama tayi ta yi masa godiya, kamar ta shige cikin sa. ***** Nasir ya dawo daga aiki, ya ga manyan motici suna shiga street ɗin su, abin ya bashi mamaki, ya ƙarasa da motarsa, ya ga a ƙofar gidan su, suka yi parking. Abbu ne ya fara fitowa, mamaki ne ya cika Nasir, ya fara tunanin a ina ya san fuskar nan, Alhaji mu'azzam ma ya fito, hannunsa riƙe da waya. Sauran motoci biyun convoy ɗin Alhaji mu'azzam ne. Ya fito daga tasa motar, a dai-dai lokacin da Baban su Nabila ma ya fito. Ya ƙarasa suka gaisa da su, Alhaji mu'azzam ya ce "Yauwwa dama baban naka nake kira, na gaya masa zan zo masa da baƙi yau" Nasir ya ce "Masha Allah, tun da ya san da zuwanku, bisimillah mu shiga" Suna ƙoƙarin shiga, sannan Viper ya fito daga mota, ɗaya daga cikin sauran motocin. Nasir yana jinjina tsabar taƙama da jin kan Viper, shi ba kowan kowa ba, sai a yanzu ya gane in da yake tunanin sanin Abbu, kamarsa ɗaya da Viper, sai ya lura irin tafiya ɗaya yake yi da mahaifinsa, sai dai shi harkar daba ce ta ƙarawa tasa tafiyar taƙama. Major na jin sallamar baƙi a falonsa, ya miƙe cikin farinciki yana yi musu maraba, sai dai yayi tururs da ya gansu tare da Bashir. Fuska babu walwala ya ƙarasa karɓar su. Alhaji mu'azzam ya yi gyaran murya ya ce "Duk da baƙin naka, wasu sanannu ne, wasu kuma baka sansu ba, wannan shi ne mahaifin Al'amin Viper, wanda ya auri 'yar uwar Nabila, wannan kuma Al'amin, wannan kuma baban su Nabila, kamar yadda ka sani. Mun zo ne a tare da shi, mu sake baka haƙuri a kan abin da ya faru, dan Allah kayi haƙuri ya wuce, ko dan samun nutsuwar ita yarinyar". Major ya kalli Alhaji mu'azzam ya ce "Ka kuwa san abin da yayi mini? Har duniya ta naɗe ba zan manta ba. Babu ƙoƙarin da ban yi ba na yafe masa na manta, amma na kasa, mussaman idan ina tuna yadda yarinyar nan ta mutu da sunansa a bakinta, duk tsananin kunyar bafulatana, amma ba ta son laifinsa, sosai take nuna son mijinta, amma ta wulaƙanta mini yar uwa ya tozarta ta, ya barota a dajin Allah ba ta san kowa ba sai shi. Na bashi yarinya amma ya aurawa ɗan daba ya kasheta" Alhaji mu'azzam ya ce "Ashsha! A bar tuna baya major, shi fa yaron nan da ka ke magana a kai, ga shi a zaune a gabanka, ga mahaifinsa ba zai ji daɗin ka din ga jifansa da irin wannan maganganun ba. Ni nan ni na fara neman auren Jauhar, Allah bai yi ba ta auri Aminu, amma zan iya ce maka, a duniya jauhar ma da ƙaunar mijinta ta bar duniya, saboda yar uwatta da na aura, kan yi zancenta da rayuwar gidanta. Kawai sharrin yan siyasa ne da rashin ji da yayi tsautsayi ya faru, idan zan gaya maka gwagwarmaya da wahalar da ya shiga bayan mutuwarta, to a matsayinka na uba, sai ka zubar da hawaye. Nabila dai ita ce da ta shiga rayuwarsa ta taimake shi, Al'amin ba ƙashin yarwa bane ba, amma ka yi binciken ka kaima, kar laifin mahaifinsu ya shafe shi dan Allah" Abbu yayi gyaran murya ya ce "Ranka ya daɗe, ita duniyar guda nawa take, duk da Alhaji Bashir yayi mini bayanin komai, bai ishe mu darasi da mamaki, ace duk da ka nesanta yaran biyu, da juna Nabila ta afka rayuwar Al'amin ba tare da ta san waye shi ba? A duniya ina gaya maka idan mutum bai yi dacen mace ba, sai addu'a kawai. Ka ganni nan, da sanya hannayena bibbiyu, a lalacewar ɗa na, bayan mutuwar mahaifiyarsa na auri ƙawarta, ina saka ran ta kula mini da 'ya'ya, amma a ƙarshe saboda makirci irin na ɗiya mace, sai da ya zama tsakanina da Al'amin babu jituwa, kamar maƙiyina, dan Allah a bar tuna abin da ya wuce" Bashir ya ce "Maitama na san duk abin da zan gaya maka, ba yadda zaka yi da ni ba, amma a irin yadda na auri Chubaɗo na fara rayuwa da ita, ka san ban aureta dan na cutar da ita ba, ƙaddara da makircin mata, ya sanya abin da ya faru ya faru, tun da ko da na aureta ka san ba mutumin banza ne ni ba. Na haɗu da sharrin mata ne da suka yi mini sihiri a kan mairamu, a gaban Nabila suka din ga faɗar abin da ya faru, amma dan Allah ka yi haƙuri, ka yafe mini" "Ba wani sihiri, dama mutum ya tara mata ya zauna ba addu'a, ba neman tsari, ba dole kowane abu ma mata su yi wa mutum ya kama shi ba" Abbu ya ce "A dai yi haƙuri, ya wuce dan Allah" "To yanzu me ku ke so?" Baba ya ce "Ina son ka bani Nabila ne, haryanzu ina kewar Jauhar, dan Allah ka bani 'ya ta" Wani mugun kallo ya yi wa Bashir, ya ce amma dai ba ka san me ka ke cewa ba ko? Nima da na rasa 'yar uwata haƙuri nayi na faullawa Allah. Kai Alhaji mu'azzam yaya muka yi da kai, ba cewa ka yi da ta kammala shari'a zaka dawo mini da 'ya ta ba? Kawai sai ku zo mini da wani zancen daban, Nabila tun da Allah ya haɗaku, duk lokacin da take so, ta je ka ganta, amma wallahi ba zan bayar ba". "Maitama kar mu yi haka da kai, ka bani 'ya ta ka tausaya mini mana" "Ita ma ka kaita su yi mata asirin kenan? Ba zai yiwu ba wallahi, kuma kai Alhaji mu'azzam, kai mun yi da kai zaku dawo mini da 'ya ta ai". Alhaji mu'azzam ya ce "Haryanzu da sauran issue ne, amma za ta dawo, tun da ai haryanzu tana zuwa nan ɗin" Abbu ya ce "Amma dai muna fatan ka yafe masa, a manta da abin da ya faru a baya?" "Ya wuce, mantawa kuma wannan ba lallai ba, 'ya kuma a ƙyale mini 'ya ta, Allah ya sa mu dace" Alhaji mu'azzam ya ce "Hakan ma Allah ya saka da alkhairi, kuma tun da ka ce duk lokacin da take so taje taga mahaifinta, Allah ya saka da alkhairi ya huci zuciyarka" Major ya numfasa ya ce "Amin" Baba ya tashi ya ƙarasa ya miƙa wa Major hannu, ya ce "Ina ƙara neman afuwarku da ahalinku, a kan abin da nayi muku, ku yi haƙuri ku yafe mini" Major kamar ya maze, ya haƙura ya miƙa masa hannu suka gaisa, Abbu ya din ga Alhamdilillah, Allah ya ƙara muku fahimta. Viper kuwa dama tun da suka fara hayaniya, ya fice ya koma ƙofar gida. Major ya ce "Bari na kira muku mutanen gidan ku gaisa, da mariƙiyar Nabilan" Ya tashi ya sauka falo, ya ce "Magajiya, ki zo ga mahaifin Nabila ne ya zo, kai Nasir ina babarku, ku zo ga mahaifin Nabila da mijin 'yar uwatta ku gaggaisa" Jikin Nasir yayi mugun sanyi, wani irin kishi da fargabar dalilin zuwan Viper da mahaifinsa ya tsaye masa. Aka gabatarwa da Baba kowa, ya din ga yi musu godiya da fatan alkhairi. Bayan tafiyar su, sannan Nabila ta dawo, ake gaya mata su Baba sun zo, ta ji babu daɗi rashin tarar da su, sai dai ta yi wa Abba godiya, jin cewar ya yafe wa mahaifinta, kuma ta san duk jajircewar Viper ce. Ta samu Abba, ta din ga yi masa godiya, da nuna masa farincikinta, a kan yafewa mahaifinta da yayi. Abba ya ce "Eh na yafe masa, amma ban yadda da maganar ki koma gidansa ki zauna ba, ban yadda da wannan ba". Nabila ta ce "Nima dama ba zan koma can ba, amma na gode sosai da sosai da ka yafe masa". Da daddare bayan ta yi sallar isha'i, ta kira Viper, yana ganin kiranta ya ɗaga, ta ce "Hello Vi" "Mmm" "Ashe kun zo gidanmu bana nan, baka gaya mini zaku zo ba, da na dawo da wuri, naga shiryawar Baba da Abbana" yayi shiru bai ce koma ba. "Na san wannan duk ƙoƙarin ka ne, na gode sosai da sosai, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi, Allah ya jiƙan 'yar madara da jaririnta, ya baka abin da ka ke nema duniya da lahira na gode, na gode" "Godiyar ta isa haka, nima na gode" "Ba ta isa ba Vi, ban san me ma zance maka, da zai tabattar da irin godiyar da nake son yi maka ba, na gode sosai da sosai" "Nima na gode sosai " "Tom sai da safe" "Nabila" "Na'am" "Haryanzu kina nan a kan bakanki ha zaki aure ni ba?" "Dan Allah mu daina wannan maganar Vi, a wuce ta dan Allah, ni na riga na gaya maka matsayata, mu yi haƙuri da wannan maganar" Ya ce "Ok, babu laifi" ya katse kiran wayar. ***** Walid ya warke sarai, hannu ya miƙe, sai dai da Viper ya yi masa zancen Abbu zai ɗauke shi, a kasuwa a nuna masa harkar kasuwanci, sannan ya bashi jari, a fara maganar aurensa da Shahida. Walid ya kasa magana yayi shiru yana kallon Viper. Viper ya ce "Menene kuma? Ko ba wannan sana'ar ka ke so ba? Idan da wani abun da ka ke so ka faɗa, sai a san abin yi" Walid ya ce "Anya gatan nan bai yi mini yawa ba Mai zamani? A bani jari kuma a bani auren 'ya?" "Ware, ka cancanci fiye da haka mai laya, yanzu yakamata mu je ko wurin ƙannen mahaifinka ne, saboda su nema maka auren Shahida, ni kuma zan je Lagos ne aiki" "Lagos kuma mai zamani, babu kai babu ɗan mama" Al'amin ya numfasa ya ce "Tafiyata can na cigaba da aiki, ya fi alkhairin zamana a nan. Dama na yi zaton ko Nabila zata aure ni ne, amma ta ce ba ta so na, dan haka zan yi tafiyata kawai, na yi aikina na fi samun kwanciyar hankali da manta wasu abubuwan" "Viper, daga kai har Nabila kuna son junanku, kawai dai rashin fahimta ne. Kaga Jauhar a sadaka ka auret, baka san duk wata wahala da ake sha, wurin neman aure ba. Yanzu ne zaka yi fafutuka da gasken gaske, idan ba haka ba ka bari ta auri wani babu lallai ka iya jurewa" "In biye mata tayi ta wulaƙanta ni?" "Ba wulaƙantaka take yi ba, kai ka fara watsar da tayinta a farko, ka din ga nuna mata da farko, an ce mata ba sa mantuwa, amma ka yi haƙuri ka nemi aurenta, Abbu ya nema maka Aurenta" Viper dai yayi shiru bai ce komai ba. ***** Major ne ya kira Nabila, ta same shi a ɗakinsa, ya ce "Yauwwa babanki ya turo mini baban yaron nan da ya auri 'yar uwakki, wai yana son ya aure ki, zasu kawo kuɗin aure, na ce sai na yi magana da ke, kina ganin kin yarda da nutsuwarsa a yanzu zaki iya aurensa?" Nabila ta yi shiru. "Magana fa nake yi miki Arfa" "Gaskiya Abba ni ba zan iya aurensa ba" "Saboda me?" Ta girgiza kai ta ce "Ni dai kawai a bar maganar nan, ka ba su haƙuri" "To uban meyasa ki ka gayyato shi rayuwarki, so ki ke ace ni na zigaki ko?" Ta girgiza kai alamar a'a. "Tashi ki je, Allah ya shiryeki" ta tashi sumi-sumi, ta tafi sai dai kuma haka kurum ta din ga jin tausayin Viper. Sumayya ta kira take labarta mata abin da ya faru, Sumayya tayi shiru, ta ma rasa me za ta ce mata. "Sumy ya ki ka yi shiru?" "Nabila me zan ce miki, abin da ki ka yi zalunci ne, ya za ayi ya sakankance, yana sonki zai aureki, amma ki ce ba kya son sa?" "Point of correction, nake son sa dai, amma ba yake so na ba" Ƙarshe sai da suka kusa yin faɗa, suka rabu tsiya-tsiya a wayar. Sumayya da kanta ta kira Abbu, suka gaisa ta fara bashi haƙuri, a kan abin da Nabila tayi. "Bakomai kar ki damu Sumayya, ai macece idan ma tayi haka ba tayi laifi ba, na san halin kayana sarai" "Abbu Nabila na ganin Ba ya sonta ne, kawai dai zai aureta saboda tana kama da jauhar ne" Abbu ya ce "Na fahimceki, ita ma kuma haka, yanzu dai zan ba su lokaci, shi kansa ya zuciya yanzu haka yana hanyar Abuja, can aka kai shi ba Lagos ba kuma, ya ce auren ma ya haƙura, amma ta nan ɓangarenki, dan Allah ki ɗan lallaɓata, ni idan ta kama ma sai na zo da kaina, ba zan so ya tafi yaje ya zauna haka babu auren ba" Jiki a sanyaye Sumayya ta ce "To shikenan Abbu, in sha Allah" Ta sake kiran Nabila, tana gaya mata yadda suka yi da Abbu. Nabila ta kada baki ta ce "Dan Allah Sumayya ki ba wa Abbu haƙuri, ba wai ina ƙyamar ɗan sa bane ba, amma ina yi masa fatan alkhairi a duk in da yake, Allah ya bashi mace madadin Jauhar". Ayshercool 08081012143 102 A ƙule Sumayya ta ce "Kina ganin hakan da ki ka yi shi ne dai-dai? A gidan uban wa ki ke tunanin zai samo madadin matarsa? Ke kin san baki isa ki ƙi aurensa ya bari ki zauna lafiya ba" Nabila ta ce "Lafiya ƙalau zan zauna in sha Allah, kar ki damu da ni Sumy, Allah ya nuna mini aurenki" "Nabila kar ki mayar da abin nan wasa, ya ki ke tunanin mahaifinsa zai ji, kin yi rejecting ɗin ɗan sa?" Sumayya, wai kina ina lokacin da na din ga gwagwarmaya, ina nuna wa mutumin nan so yana wahalar da ni?" "Ramawa ki ke kenan?" "Da zan rama abin da Vi yayi mini, ko kallonsa ba zan iya yi ba, kawai dai ba zan aure shi bane" "Munafuka, kina wani kiransa Vi, kina wulaƙanta musu ɗa, nan ki ka roƙi Allah ya baki kowane irin miji ne, mutum ya nuna yana sonki, amma kina wahalar da shi, zaman gidanku da wannan cin mutuncin ne da ake yi miki bai ishe ki ba, ki ƙarata" Nabila ta ce "Bakomai, na ji na yadda" **** Alhaji mu'azzam ne a ƙofar gidan su Hafsa, ya fi mintuna ashirin yana surutu, amma Hafsa ta yi masa banza ta ƙi kula shi. "Hafsa" ta ɗago ta kalleshi. Ya ce "Meyasa ba zaki yafe mini ki koma ɗakinki ba?" "Meyasa zan koma in da ba a buƙatata? Gara na barka waɗanda kake ƙauna". Ya ce "Na san ban kyauta ba, amma ki yi haƙuri, zan gyara kuskurena" murguɗa baki tayi, ta sake juya masa baya. Murmushi ya yi a ransa ya ce "Komawar ki gidana ita kaɗaice mafita a garemu baki ɗaya" a zahiri kuma ya ce "Shikenan sai da safe" Ba ta kula shi ba, kawai ta shige cikin gida ta bar shi a wurin. Yayi murmushi ya furta mace kenan, duk yadda ake ganin girmansa da mutuncinsa a ƙasa, yana ta bin yarinya ƙarama tana wana shi. **** Viper ne a tsaye a banɗaki, ya sakarwa kansa ruwa, a hankali ya kammala wankan ya fito, jikinsa duk babu ƙwari. Ya shafa mai, yayi shirin kwanciya bacci, gaba ɗaya abin da Nabila tayi sai cin zuciyarsa yake yi. Yana jera kayansa a cikin wardrobe, yana tuna tarbiyyar Jauhar ce, da ta hana shi watsar da kaya ko ina, duk yadda ya ga dama, da har ta koya masa rashin son baza kaya ko ina. Ɗan ƙaramin hotonsu ne shi da ita ya faɗo, ya durƙusa ya ɗauka ya zauna a gefen gado yana kallo. Kamaninta sun ɓaci da ita da Nabila. Ya kalli jikinsa, ya tuna yadda komai dare idan ya gama yawonsa ya dawo, sai ta haɗa masa ruwa mai zafi yayi wanka, tun ba ya so bar ya zo ya saba, ta shafe shi da mai sannan ya kwanta bacci. Gashi ba ta taɓa gajiya da duk wata rigimar sa, sai dai idan yayi mata laifi, to fa ba ruwan wanka, balle shafa mai da tausa, hirar ma ba zata yi masa ba. Kayan shafe-shafen gyaran fatarta kuwa, wataran haka take zaunar da shi, shi ma ta shafa masa wai yayi kyau. Ya ɗan saki murmushi ya ci gaba da kallon hoton, ya ce "Kin bar ni da tabo mai tsananin zafi a cikin zuciyata, sai wahala nake yi, ga twin sister ɗinki ta ce ba ta so na, ke kaɗai ki ke so na babyn robana" yayi maganar kamar taɓaɓɓe. Ya nemi wuri ya kwanta, rayuwarsu ta baya na dawo masa, Addo'in kwanciya bacci, ita take yi masa idan bai yi ba, yawan yi masa ya sanya ya haddace su tsaf a kansa. Ya tuna ranar da tana cikin yi masa addu'a, ta idar ta tofa masa, ta shafa sumarsa ta ce "Mai zamani, yaushe zamu je aski ne?" Ba shiri ya buɗe ido ya ce "What me ki ka ce?" Ta hau dariya ta ce "Viper" "Viper ko?" Yayi maganar yana matsa kumatunta. Cikin shagwaɓa ta ce "Sorry yaya master" "In sake jin ki faɗi wannan sunayen, ni da ke ne, matso to rarrashe ni na yi bacci, ki sake yi mini wata addu'ar" "Naƙi ɗin, tun da ka ci zalina, ka san dai ka fi ni ƙarfi, amma ka matse mini kumatu" Ya ce "Eyya, to ni zo na rarrasheki ki yi baccin " "A'a ba na son wannan rarrashin, mun yi faɗa, yau ina farkon gado, ina ƙarshe" Yayi dariya yana gyara kwanciyar sa, ya ce "Da shegen son jikinki, ina nan zaki mirgino ki same ni ne" Ta riga shi yin bacci, aka kawo wuta unexpected, ya ashe ƙwan ɗakin a kunne yake, ya tattara nutsuwar sa, da hankalinsa a kanta, bacci take yi sosai, da alama baccin gajiya ne, dan har alarm ɗin ta ya buga na lokacin sallar dare, ba ta sani ba. Ya tashi ya je ya sha ruwa, ya kashe fitilar ya kwanta, ya rungumeta a jikinsa, yana jin wani irin abu game da ita, na mamaye kowane sashe na zuciyarsa. Cikin magagin bacci ta ce "Master" Ya ce "Mmmm" "Ya Allah ka shirya mini shi, Allah ka yaye masa wannan shaye-shayen, Allah kar saka ya dawo gareka yana aikata ɓarna, Allah ka bashi halal, ka bashi juriya da jarrabawar rayuwa. Allah ina son mijina a haka, Allah ka sanya yana da rabon shiriya" a cikin bacci take ganin kamar tayi salla, take ta jerin wannan addu'oin a fili. A hankali ya dawo daga tunanin da yake yi, ya kalli hoton ya ce "Wannan ce juriyar da ki ke roƙa mini, juriyar rashin ki 'yar madara" ya ajjye hoton ya canza kwanciyarsa, yana jin yadda zuciyarsa take yi masa zafi. Bacci ne ya kwashe shi, sai dai yau a maimakon Jauhar, da Nabila yayi mafarki, cikin yanayi na ma'aurata, ko da ya farka ya makara sallar asuba, tsaki ya yi ya tashi, tare da furta jarababbiya, ko meya kawo ta baccina" Ta ƙarfin tsiya yake son sanya wa kansa jin haushin Nabila, amma abu ya gagara, wata irin kewarta ce ma take damunsa, gaba ɗaya tunanin mafarkin da yayi, yaƙi barin kansa. Wato nutsuwa da kwanciyar hankali ba abin da ba ya sanyawa, a lokacin da yake cikin ha'ulai'in tashin hankali, ko kusa baya wani tunani, balle ya kwanta ya yi wani mafarki, ba ma haka ba, baccin ma ba iya yin sa yake yi ba, balle yayi wani mafarki. Yanzu kuwa hankalinsa a kwance yake a cikin nutsuwa, ya shirya ya auri Nabila da zarar komai ya daidaita, saboda ya san yana buƙatar hakan, amma lokaci ɗaya ta hau dokin naƙi, wai ba ta son sa. Ɓangaren Nabila ma, yanzu zaman gidan major bai fiye yi mata daɗi ba, duk sun ƙara tsangwamar ta, yanzu ta fi zama a barrack, ta fi jin daɗin zaman wurin madam, sai dai kuma da an kwana biyu sai ta ji gida take son komawa. Tana zaune ta idar da sallar asuba, ta yi azkar, ta kifa kanta tana ƙarasa azkar ɗin, bacci ya kwasheta, dan kuwa yanzu bacci rabi da rabi take yin sa, saboda tunanin halin da Viper yake ciki, tana ta addu'a da fatan Allah ya sa kar ya koma halinsa na da. Kawai tayi mafarkin farkon haɗuwarsu da Viper, a lokacin da yake Vipern sa, tamkar mahaukaci, ya soka mata wuƙa a ciki.  Ihu ta kurma ta tashi tsaye tana dafe cikinta. Baba magajiya ce ta shigo ɗakin a razane, Abba yana daga saman benensa ya jiyo ihunta, sun saba da irin wannan ihun na Nabila wasu lokutan, amma kwana biyu tayi lafiya. A sukwane ya saukko shi ma, ya shiga ɗakin nata, ya tarar baba magajiya ta riƙeta, sai kuka take tana riƙe cikinta, tana dubawa ko zata ga jini. "Menene kuma?" "Viper ne ya caka mini wuƙa, a kai ni Asibiti" "Wane Viper kuma, kalli dai a ina ki ke?" A hankali take ƙarewa ɗakin kallo, ta kalli jikinta ta ga lafiya ƙalau. "A garin shegen kwashe-kwashen ki, kin kwaso abin da zai hanaki bacci, bayan kwaso masu farautar rayuwarki, kin yi azkar ma kuwa?" Ta jinjina masa kai, ta nuna masa wayarta da sautin karatun Alqur'ani yake tashi ƙasa-ƙasa. "Nemi wuri ki kwanta ki huta" ta ƙarasa kan gadon, tana ajiyar zuciya. A ranta ta ce "Vi fushi ka ke da ni har haka?" ta lumshe idanunta, ƙirjinta na ci gaba da bugawa cike da matsanancin tsoro. Wajen ƙarfe sha ɗaya na rana ta gama shirinta, ta fice zuwa wurin aiki. Tana zuwa ta tarar da Walid tare da Liti suna jiranta. Cikin mamaki ko gaisawa ba su yi ba, ta ce "Allah ya sa lafiya na ganku, ba wani abin ne ya same shi ba ko?" Walid ya ce "Kwantar da hankalinki, babu abin da ya same shi, yana nan ƙalau" Ta ce "To Alhamdilillah" ta jagorance su zuwa cikin ofishinta, bayan sun gaisa Walid ya ce "Na san zaki yi mamakin zuwanmu, duk da ba abin mamaki bane ba, amma dole ki ganmu. Nabila dan Allah me Viper yayi haka ki ke wahalar mana da ɗan uwa, kin san komai zai iya faruwa ƙin auren nan nasa da ki ka yi, idan ba ke ɗin ba wacece zai je ya aura su zauna lafiya?" "Ni ɗin ma babu lallai mu zauna lafiya" ta bashi amsa. "Amma meyasa ki ka ce haka?" Nabila ta ce "Halin Viper ai sai dai Jauhar ɗin, kuma ma duk ba wannan ba, gani nake cik amana ne kamar ban kyauta ba, ace na auri mijin Jauhar, dan Allah ku yi haƙuri, ku bashi haƙuri, na san a fusace yake da ni, tun da nayi mafarkinsa yana caka mini wuƙa" Walid ya ce "A'uzibillah lallai kam ya tabatta Mai zamani yana fushi da ke, amma dan Allah ki yi tunani, ki taimaki rayuwar ɗan uwanmu" "Oga Walid ina jin kunyarka, dan Allah mu bar wannan maganar" Walid ya ce "To shikenan, amma dai dan Allah ki yi tunani a kai" Nabila ta yi murmushi ta ce "To Oga walid in sha Allah za ayi" Ɓangaren Viper kuwa, abu kamar wasa, ya damu da rashin Nabila sosai da sosai, wasu lokutan sai ya shiga what's app ɗin sa, yana sauraren Voice message ɗin ta. Gashi ba yau ba gobe cikin mafarkinta yake, abin har ya fara bashi tsoro, domin kuwa abin ya fara yawa. Tabbas yana buƙatar sake yin wani auren, dama Nabilan ce ya saka rai, kuma gashi ta ce ita ba zata aure shi ba. **** Kwanci tashi asarar mai rai, Abdul ya cika wa'adin da aka ɗebar masa, na zaman gidan yari, tun safe mahaifiyarsa ta haɗa motoci ta tafi ɗaukar sa. Ɓangaren ramma ma ji take yi kamar salla, saboda a lissafinta yau ne fitowar Abdul, sai dai Nabila ba ta ce masa komai ba. A ɓangaren sa ma Abdul ɗin, murna yake yi na fitowarsa, ko ba komai ya fuskanci ƙalubale na gaba, na samun damar ci gaba da rayuwa da matarsa, kuma gashi ya fito dag da lokacin cikar EDD ɗin ta. Ramma ta kasa zaune ta kasa tsaye, mama ta fara bacci, ta ɗauki wayarta, ta tafi ɗakinta ta rufe ƙofa, ta kira lambar Abdul. Cikin sa'a kawai ta ji muryarsa. "Doctor" "Babyna da wayar wa ki ka kirani?" "Shi ne ka fito ko ka neme ni, ina ta zullumi da lissafin yaushe zaka dawo?" "To ta ina zan neme ki, ba waya a hannunki yanzu, ni kuma tun da na dawo Mummy ta kafa ta tsare, ba zata bari na fita ba, amma kina raina wallahi, EDD ɗinmu ya kusa cika ko?" Ta ce "Eh, duk na gaji wallahi, cikin yayi mini nauyi, na ƙagu na haihu na huta" "Dan Allah kar ki saka damuwar sai kin haihu abin ya dame ki kin ji sweetheart?" "To doctor, ka huta lafiya" "Ina batun hutu, na so da na dawo a gidana zan zauna, in ci abincin da ki ka dafa, mu kasance tare cike da so da ƙaunar juna, na yi missing ɗinki da yawa fa, yanzu dai ga abinci ga komai, amma duk ba wannan nake buƙata ba, ke nake buƙata a kusa da ni" "Kaga sai anjima, ba zaka yi wannan zancen da ni ba" "Au haka ma zaki ce, shikenan anyway in sha Allah a satin nan duk yadda ake ciki, zan zo na ganki" Suka yi sallama cike da kewar juna. Abdul ya saka ranar da zai zo ganin rahama, sai dai ta rasa yadda za ta sanar wa mama, gani take kamar ba zata yadda ba. Dan haka ta kira Nabila ta gaya mata, Abdul yana so ya zo ya ganta, ko zata gaya wa mama, ita tana jin tsoron ta gaya mata, Nabila ta ce ba damuwa. Ta kira mama a waya, suka gaisa Nabila ta ce "Mama, mijin rahama zai zo ya ganta, zai ga kayan sayayyar da na yi mata, da kuma yanayin jikinta, ina fatan ban yi laifi ba, na bashi adress na ce ya zo nan gida" Mama ta ce "Mhmm ba ki yi laifi ba, ba wani abu" "Yauwwa mama na gode sosai, a ci gaba da haƙuri dai dan Allah" Ta ce "Ba komai" Ramma da ciki ya sanya, wataran idan tayi wanka, ko mai ba ta shafawa, amma mama na kallonta, har da su fesa turare, da saka kwalli da shafa man leɓe mai kala, ita dai ba ta tanka mata ba ta rabu da ita. Yaro ne ya shigo, ya ce "Wai Abdul ya zo yana waje" Ramma ta ce masa "To ana zuwa" ta saci kallon mama, taga tayi banza da ita, ƙarshe ma ta tashi ta bar falon. Hakan ya bata damar tashi tana jan ƙafa da kyar, ta fita harabar gidan. Yana tsaye cikin yadi ash, kansa babu hula, ya goya hannunsa a bayansa yana kallon gidan, yana jinjina wa Alhaji mu'azzam, ya taimaki su ramma, mussaman da ya tuna gidansu na ƙauye da ko ƙofa babu. "Me ka ke kallo ne?" Ya juyo ya kalleta. Duk ta kumbura ta cika, ga uban ciki tana ja da kyar, hangowa yayi kamata yayi ace tana makaranta, ko idan cikin ne, ace a gidanta na aure take, gaba ɗaya sai jikinsa yayi sanyi. Ya kalleta ya ce "Sannu uwar biyu" Ta harare shi ta ce "Wane irin biyu kuma? Ɗayan ma ya aka ƙare, sannu da zuwa. Lallai prison ta karɓe ka, ka ƙara haske sosai ka yi kyau" "Hmm ina daɗi a prsion, ke dai ayi sha'ani kawai" Ramma ta yi masa jagora, suka ƙarasa cikin sitting room ɗin da yake harabar gidan. Ta shiga cikin gida, ta ɗaukko masa abincinta, da ruwa da lemo ta kawo masa ta ajiye. Tana ta ƙoƙarin yadda za ta juya ta zauna, kawai ya zaunar da ita a cinyarsa. Riƙe cikinta tayi ta ce "Wayyo Allana, kai ba ka ga halin da nake ciki ba, da na bige ciki fa?" "Haba dai, na san abin da nake yi ai, na fiki son cikin nan fa" ya ɗaga rigar jikinta, cikin nan yayi girma sosai da sosai. Cikin matsanancin shauƙi da ɗokin son ganin abin da zata haifa, ya ce "Sannu your excellency, Allah ya raba ki da cikin nan lafiya, na gode Allah da na fito kafin haihuwar ki, ni zan karɓi haihuwar nan, na rigaki ganin babyn" "Taɓ, a'a gaskiya, ba zaka karɓa ba, ni wallahi tsoro ma nake ji" Abdul ya ce "Ba wani tsoro, ki kwantar da hankalinki, ai na san ke mai yawan ibada ce, mu yi ta addu'a Allah ya sauƙaƙa miki. Yaushe zamu je sayayyar kayan baby ne?" "Ka manta mun sayo ni da Anty Nabila, Alhaji mu'azzam ma ya sayo wasu ya kawo" Abdul ya ce "To Allah ya saka da alkhairi, Anty Jidda sun haɗa kai da Mummy, suna ta yi mini faɗa, saboda ke wai ba ni da zuciya, ni kuwa in dai a kanki ne, ba zan yi zuciya ba duk tsanani, ni dai a bar mini ke, mu yi rayuwar aurenmu cikin kwanciyar hankali". Ramma ta yi shiru ba ta ce komai ba, ya numfasa ya ce "Zuba mana abincin mu ci tare, ina fatan dai ke ki ka dafa?" Ta jinjina masa kai, tare suka ci abincin, sai dai sai da ya so ya wuce gona da iri, ramma ta ankarar da shi a in da yake. Ya ce "Rakani mu je na gaida mama" Sai da ta ɗan yi jimm, sannan ta shiga gaba ya biyota a baya, aka yi sa'a maman tana falo a zaune. Abdul ya shiga da sallama, ya durƙusa har ƙasa yana gaisheta, ta kawar da kanta gefe sannan ta amsa masa. Daga haka ya miƙe ya ce "Na tafi to, sai anjima" Mama ta ce "To ka gaida gida" Da suka fito Ramma tayi zaton zai nuna ya ji babu daɗi, yadda ta amsa masa, amma bai nuna mata ba, sayayyar da ya yi mata ya bata, yayi mata sallama ya tafi. Ramma ta kasa gane kan mama, haushinta take ji ko kuma yaya, gaba ɗaya ta ɗauke mata. Abdul yana son kiran waya yayi magana da ramma, amma ta ce kar ya kira wayar mama ce, shi kansa shakkar ramman yake ji. Kotu ta bayar da umarnin a kamo Naja'atu Bunkure, tun da taƙi gurfana ta kare kanta bisa ga tuhume-tuhumen da ake yi mata. Viper ya dira a garin Kano, da misalin ƙarfe huɗu na yamma, a can gidansu da suke zaune yaje ya sauka, ya tarar daga Walid har liti duk ba sa nan, yayi wanka ya huta, sannan ya shirya ya tafi cikin gari. Ya tarar Abbu baya nan, kawai Rahila ta fito ta ce "Sannu munafi mara mutunci" ya tsaya yana kallonta. "Eh, na ce sannu munafuki, saboda algungumi ne kai, baka tsoron Allah, shi ne ka haɗa kai da babanka, zaka aura wa Shahida ɗan iska kamar ka, to baka isa ba, Shahida gidan tsohon mijinta zata koma" Viper kamar ya tanka mata, amma sai ya rabu da ita ya fita. Yana nan a ƙofar gidan daf da magariba, sai ga Abbu ya dawo, tare da Walid, Walid ne yake jan motar, Abbu yana gaba suna hira. Walid ya din ga yi wa Viper horn,ya taso ya nufo su, Abbu ya ce "Ya aka yi ka dawo kuma? Ni na yi ɗa dama baka dawo yanzu ba" Viper ya yi murmushi ya ce "Ai ba daɗewa zan yi ba, yanzu ma idan aka ce na koma tsaf zan tafi" Abbu suka fito daga motar, Walid ya ba wa Abbu mukullin ya ce "To Abbu sai Allah ya kaimu gobe" Abbu ya ce "A'a, kira wo mini Abdallah a waya, ya ƙaraso shi ma ku ci abinci tukuna" Suka yi alwala, suka je suka yi sallar magariba suka dawo, suka yi shimfiɗa a ƙofar gida suka zauna, har ƙarfe tara na dare suna tare, wajen tara da rabi, Viper ya ce su tafi zai taho. Abbu ya din ga bawa labari jin daɗin zamansa da Walid, saboda biyayyarsa da riƙon amana, kuma ya ga sun fuskanci juna da shi da Shahida, dan haka baya son a wani ɓata lokaci, saboda Rahila na ƙoƙarin ɓata lamarin. Haka suka cigaba da tattauanawa, a kan yadda shirin bikin zai tafi. Liti kuwa Alhaji ya ce sai ya koma makaranta ko per time ne, sannan kuma zai kai shi kasuwa. Liti ya ce "Amma dai da daddare idan na dawo, an je rumfar shayi" "Wai rumfar shayin nan, ba cewa aka yi kayan shaye-shaye kuke sayarwa a ciki ba?" "Wallahi mun daina sayarwa, harkar shayi da indomie da sauransu ake yi a wurin, kuma wannan rumfa tana da tarihi domin tunawa da marigayiyya Jauhar matar Viper, ba zan bari rumfar nan ta mutu ba. Kuma a yanzu haka wallahi yaranmu sun kai biyar da suke cin abinci a wurin, ni kula nake yi da ita, akwai amana ai, duk in da na je da daddare sai na je rumfar nan" Alhaji ya ce "To, Allah ya tallafa" Ya amsa da Amin. *** Kwana na biyu kenan ramma ramam tana ta zubar da ruwa, ta rasa yadda za ta yi, gashi mama yanzu ba wani sakar mata fuska take yi ba, dan haka ba ta gaya mata ba, ba ta zata hakan wata matsala ba ce, dan haka ta ja bakinta tayi shiru. Sai da Nabila ta bushi iska, ta je gidan, take gaya mata, Ba ƙaramin ƙuluwa Nabila tayi da abin da mama take yi ba, ta karɓi lambar Abdul, ba tare da ta saurari mama ba, ta kira shi ta sanar masa, a sukwane ya ce gashi nan. "Ina zaka je kana zauna kana cin abinci kuma?" "Mummy asibitina zani, aikin gaggawa ne ya taso" "Yaushe ka dawo har ka koma aikin da zaka ce mini wani aikin gaggawa? Da da kake tsare waye yake aikin?" "Ki yi haƙuri na je na ji menene" ya ajiye cokalin ya yi gaba. Ya kira lambar Nabila ya ce ta ɗaukko ramma su haɗu a asibitinsa kawai. Nabila ta fito falo ta ce "Mama zan tafi da ramma asibitin royal, can asibitin mijinta, ba ta da lafiya ya ce lallai a kaita shi ma ya tafi, kwana biyu tana zubar da ruwa" Sai kuma ta tashi a kiɗime, ta ce "Ramma naƙuda ki ka fara baki gaya mini ba?" Ramma tayi shiru, ta ce "Ai akwai tofinta, da kayan haihuwa da na haɗa, ko da su za a tafi, ko haihuwar ce?" Nabila ta ce "A'a bari muje kawai, tun da ba ciwo take ji ba, idan haihuwar ce sai muyi waya ki taho" "A'a ba haka za ayi ba, mu tafi kawai bari na ɗaukko mayafina" tana shiga ɗaki, sai ma ta rasa wa zata kira, kawai ta kira Viper tana gaya masa. Ya ce "Ai yau da daddare nake son zuwa da ni da Abbu ku gaisa, amma gani nan zan biyoku asibitin" Ko da suka je asibitin, a harabar wurin suka tarar da Abdul, yana ta kaiwa da komowa, suna isowa, ya nufe su, Nabila ta kamo hannun ramma, ta fito daga cikin motar, tana takawa da kyar, duk da ta saka pad, amma ruwan da take zubarwa duk ya ɓata mata jiki. Wheel chair ya ɗaukko da gudu, ya ajiye suka ɗora ramma a kai, ya tura ta cikin asibitin. Tuni ya kira doctor Muktar, wanda abokinsa ne, kuma shi ya yi wa ramma awo. Bayan fitar Abdul, doctor Muktar ya yi wa ramma scanic, ya kalleta ya ce "Yaushe rabon da cikin yayi motsi?" Ta ɗan shiru ta ce "Tun jiya da safe" Abdul ya dawo ya ce "Muktar, yaya ake ciki ne?" Ya gyaɗa kai ya ce "Low amniotic fluid, a shirya OR kawai, ayi mata EMCS" Ya ce "Ya subhanallah, amma ya babyn" ya faɗa a rikice. Muktar ya ce "Meye haka? Wato saboda wannan taka ce shi ne zaka wani ruɗe? Dan Allah ka nutsu mana, normal in sha Allah, ka shirya ka yi assiting ɗina, sai a ciro babyn, ka kira anesthetic ɗin" "Abdul meya same ni?" Tayi maganar kamar zata yi kuka. Ya ƙarasa ya riƙe hannunta, ya ce "Ki kwantar da hankalinki, tun yaushe ki ke zubar da ruwan nan?" "Ni na manta, ka gaya mini Meya same ni?" "Ruwan da babynmu yake ciki ne yayi masa kaɗan, saboda rashin sanarwa da wuri da ba ki yi ba, duk ruwan ya zube, yanzu tiyata zamu yi miki a ciro shi" Ramma ta fashe da kuka ta ce "Yanka ni za ayi kenan, wayyo Allah tsoro nake ji" Ya ce "Ki yi haƙuri, babu wani abu in sha Allah" Ya kalli muktar ya ce "Doctor Muktar, ko zaka yi wa mamanta bayani, suna falon office ɗina" ya jinjina kai ya fita. Doctor Muktar yana zuwa, ya tarar da Nabila da mama, ya ce "Matar master, sannu fa" "Matar master ai ta rasu" Ya ce "Ai ni duk abu daga nake gani, amma ya aka yi ta gama awo successfully, matsala ta taso ku kasa faɗa sai da ta zama worse? Kwana kusan biyu tana zubar da ruwa fa" Nabila ta ce "Wallahi ba ta faɗa bane ba doctor " Ya ce "Aishikenan, yanzu tiyata zamu yi mata ta gaggawa, amma babu wani abu in sha Allah" maman ramma ta dafe ƙirji ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yanzu ina ramman take?" "Ki kwantar da hankalinki, yanzu kafin a shiga da ita, zaku ganta in sha Allah, ke Nabila taho muje ko da abin da zaki yi mata". Suna barin wurin sai ga Viper, ya tarar da mama na matsar ƙwalla. Ya ce "Lafiya ya ake ciki?" Nan ta gaya masa abin da suka ce, a rikice ya nufi cikin asibitin, ba ya ƙaunar duk wani abu, da zai shafi mai ciki. Ba tare da ya yi knocking ba, ya shiga ɗakin, har Abdul ya sanya wa ramma rigar tiyata, ya rungumeta yana ta rarrashinta tana kuka, wai tsoro take ji. Tsit suka yi suka zuba masa ido, ramma na ƙoƙarin barin jikin Abdul. Nabila ce suka shigo tare da doctor Muktar, ya bata consent form, da za a saka hannu ayi wa ramma aiki. Doctor Muktar ya ce "Allah ya taimaki master, kwana biyu " ya miƙa wa Viper hannu suka gaisa. Al'amin ya ce "Ina ganinka gabana ya faɗi doctor Muktar, a wancan karon matata a wannan karon ƙanwata, ya ake ciki menene matsalar?" "Ahh ba wata damuwa, in sha Allah, aiki zamu yi mata, ruwan da yaron yake ciki ne yayi masa kaɗan" Ya jinjina kai ya ce "Allah ya raba su lafiya" Ya kalli ramma da fuskarta ta jiƙe da hawaye ya dafa kanta ya ce "Rahama" karon farko da ya kira sunanta, ta ɗago ta kalleshi. "Ki yi haƙuri ki kwantar da hankalinki kin ji? In sha Allah babu wani abu, za ayi miki aiki lafiya a gama lafiya, ki yi ta addu'a, ki daina wannan kukan, kar jininki ya hau" Ta ce "Yaya tsoro nake ji, yankani za ayi" "Ai ba zaki ji zafi ba in sha Allah" Nabila ta maze kamar ba ta ga Viper ba, kamar yadda shi ma ya maze. Ta ce "Ga consent form da aka ce a cike, wa zan bawa ne?" Ta miƙa wa Abdul, ya saka hannu zai karɓa, Viper ya karɓe form ɗin ya na tsareta da idanunsa, ya ciro biro a gaban rigarsa ya saka hannu. Abdul kawai ya zuba wa sarautar Allah ido. Ya ajiye form ɗin bayan ya saka hannu, ya miƙa wa ramma hannunsa, ta saukko daga kan gadon, ya kalli doctor Muktar ya ce "Ina ne ɗakin tiyatar?" Ya jagorance su, su na tafe yana tuna 'yar madara, su na zuwa bakin ƙofar mama ta ƙaraso. Ta ce "Ramma, Allah ya fito da ke lafiya, Allah ya sa ayi a sa'a" Abdul ya ƙaraso, Viper ya kalle shi, ya miƙa masa hannun rahama, Abdul ya kama hannunta, suka shiga cikin tiyata, tana yi tana waiwayowa tana kallonsu. Ayshercool 08081012143 104 Abdul ya shiga da ramma cikin ɗakin, ya taimaka mata ta kwanta a kan gadon tiyatar, ya shiga ya canza kayansa zuwa na tiyata, sai rarraba Idanu take yi, cikin matsanancin tsoro. Aka shirya ta tsaf, Abdul ya ce a kuma scanic, Doctor Muktar ya ce no need. Duk wani examination da zai yi wa ramma, sai Muktar ya hana shi, ya ce masa ya riga ya yi. Aka duba Vitals ɗin ramma, komai normal sai palpitations, zuciyarta na bugawa da sauri da sauri, suka din ga rarrashinta, suna kwantar mata da hankali. Aka yi mata abin da yakamata, aka kwantar da ita, aka ce ta ɗaga ƙafafuwan ta, ta ce ba zata iya ba, suka rufe yadda zata ga me suke yi, ta miƙa hannu ta riƙo na Abdul. Doctor Muktar ya ce "Anya ba korarka zamu yi ba, malam ka nutsu ka mayar da hankalinka mana" Ramma ba ta san me ake yi ba, ta ji kamar ana yi mata shocking dai, kuma ana jijjigata. Gashi sai surutu suke yi mata, suna mata hira mai ma'ana da mara ma'ana. Ta ce "Doctor Abdul" "Yes my dear" "Ban taɓa ganinka a cikin kayan tiyata ba, sai yau da Allah ya yi kai zaka yanka ni" Ya ce "To ya ki ka ga, sun yi mini kyau?" Ta ce "Sosai ma, duk sun fi yi maka kyau". Muktar ya ce "Ban da son kai fa, tsakani da Allah na fishi kyau" Ramma ta ce "Anya kuwa? Doctor ashe doctor Muktar ne ya yi wa Anty Jauhar matar Yaya Aminu awon ciki, kuma shi ya tabattar da rasuwarta" Abdul ya ce "Haba dai?" "Wallahi tambaye shi ka ji" Muktar ya ce "Baka ga yana ta lallaɓa rahama ba, gayen nan na tausaya masa, ko yanzu kafin mu shigo, naga damuwa a tare da shi, ana gobe za a kashe ta, na gaya masa ya tanadi kuɗi, idan inducing bai yi ba, yayi failing C.S ne, gayen nan ya ce ko nawa ne, zai nemo su, na daɗe ban ga zunzurutun so da ƙauna ba sai a wurin su, kuma kalli ikon Allah ga 'yar uwatta nan da take kawo Madam awo, kamar su ɗaya sak" Shiru Abdul yayi, bayan da Muktar ya ciro jaririn cikin rahama, jibgegen yaro, fari ƙal alama ya daɗe ma da mutuwa, fatarsa ta fara macerating, sai dai kyakykyawan gaske ne, ga gashi cunkus a kansa, har goshinsa zuwa girarsa gashi ne. Abdul ya kalli doctor Muktar, amma ya girgiza masa kai, yayi masa alamar yayi shiru. Ramma ta ci gaba da magana, doctor Muktar yana bata labarin Viper da Jauhar. Ta ce "Wai haryanzu ba a ciro ɗan ba?" "Babyn naki ne, ƙato to, amma yanzu za a ciro shi in sha Allah" Ta ce "Allah ya fito mini da shi lafiya, na bi na ɗaga hankalina, ashe CS ɗin ba abin tashin hankali bane ma" Maman ramma na can waje, tana jera salloli tana addu'a, Allah ya sa a fito mata 'yar ta da lafiya. Viper kuwa kamar ya haɗiye Nabila, sai satar kallonta yake yi, duk da ta basar da shi, amma zuciyarta azalzalarta take yi, ta kula shi, ta yi kewarsa sosai amma ta maze, ta kira Sumayya ta gaya mata suna Asibiti wurin ramma. Ramma ta ji shiru-shiru, ba a ce mata ga ɗa ba, ta ce "Nifa ban ji yayi kuka ba, idan kun ciro shi, ku nuna mini shi mana" Muktar ya ce "Ai sai mun gama, an kai ki ɗakin hutawa sannan zaki ganshi" Ta ce "Ka haɗa kai da abokinka sai ya rigani ganinsa, shikenan ai" "Wai dama kina magana haka? Kullum idan aka kawo ki awo, kanki a ƙasa kina ɓuya" Tayi murmushi ta ce "Idan na yi shiru, zai shiga damuwa ne, shiyasa nake magana" Muktar ya girgiza wa Abdul kai, saboda yadda ya karaya jikinsa yayi sanyi, ya ƙallafa ransa da ɗora buri a kan abin da ramma za ta haifa, daga fitowarsa ya sai sa da rago, saboda ya ce ko me za ayi, ko a faɗa sai dai ayi, amma babban shagalin bikin suna zai yi. Ya nananɗo jaririn a zani, ya fita daga cikin tiyatar jikinsa a sanyaye. Gaba ɗaya suka nufo shi, suna jera masa tambayoyi. Maman ramma ta ce "Yaya ina rahaman? Mutuwa tayi?" Ya girgiza musu kai alamar a'a. Viper ya ce "Kayi magana mana menene?" Yayi maganar yana ƙoƙarin karɓar jaririn. Ya karɓe shi, ya buɗe shi, ya ga bashi da rai. Take jikin Viper ya sanyi ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Yaron ba shi da rai, kamar ma ya kwana biyu da rasuwa, amma mama da wa yaron nan yake yi miki kama" yayi maganar yana nuna mata fuskar jaririn. Ta ce "Kaii, kamar Nura ce ai wannan, wallahi kamar su ɗaya sak, bani shi na gani, ina ma yana da rai, wayyo Allana" ta karɓi jaririn tana kallonsa, hanci har baka ƙato mai kyau, amma babu rai. Abdul ya koma ya jingina da jikin bango yana kallonsu kawai, jikinsa gaba ɗaya ya yi sanyi, yama kasa komawa ɗakin tiyatar. Sai da Nurse ta fito ta ce masa, ana nemansa, sannan ya shiga, ya tarar an gama ɗinketa, har an sakata bacci, aka fito da ita daga tiyatar, suka nufeta, suka tarar bacci take yi, dan yadda aka fito da ita kamar matacciya. Aka kaita post-op room, aka kwantar da ita. Doctor Muktar ya kalle su ya ce "Haƙiƙanin gaskiya, tun da ku ka zo na yi mata scanic, naga yaron ya mutu, bana son ɗaga muku hankali ne, ta ƙara karaya kafin ayi aikin, rashin sanar da batun zubar ruwan nan ne, da wuri ya ƙara ta'azarra lamarin. Amma Alhamdilillah ita tana nan ƙalau, mun tura lab ayi post-op pcv, mu gani idan jinin jikinta ya isheta normal ne, idan kuma akwai buƙatar a ƙara shikenan, amma dan Allah a rarrashe ta, a bata baki" Mama da su Nabila suka yi ta yi masa godiya. Viper ya ce "Yakamata ka zo mu je a binne shi ko" Jiki a sanyaye ya ce "Dan Allah a jira ta farka, ta ganshi, idan aka rufe shi ba ta ganshi ba, za ta ji babu daɗi" Viper ya jinjina kai, mama ta miƙa wa Viper yaron, ta tafi gaban gadon ramma da take ta bacci, tana kallonta tana shafa kanta cike da tausayawa. Viper ya riƙe yaron sosai, ya zuba masa ido, ya tuna shi ko gawar masa ɗan ma bai gani ba, kamar dai Abdul ɗin nan haka ya din ga zumuɗi a kan haihuwar da yake saka ran ayi masa, amma a ƙarshe duka biyun ya rasa su. Shirun da ya yi yana kallon jaririn, Nabila ta san me yake tunawa, saboda yadda ya tattara nutsuwar sa kacokan a kansa, yana ta sauke numfashi. Nabila ta miƙa wa Viper hannu, ta ce "Ba ni shi nima na ganshi" Mugun kallon da ya yi mata sai da ta ja da baya, ya koma gefe ya zauna, rungume da gawar yaron. Alhaji mu'azzam ba ya gari, ya aiko yaronsa da yake yi wa su ramma hidima, idan da wani abu da ake buƙata. Nabila idan idonta dai-dai yake gane mata, har da harara Viper yake ta aika mata. Abdul kuwa sai da ya zubar da hawaye, a cikin zuciyarsa yake jin ƙaunar yaronsa, gashi dai babu rai ya zo, amma sosai yake jin son sa a ransa. Mummy ce ta addabe shi da kiran waya, ya gaji ya ɗaga ta ce "Kana ina ne?" "Ina Asibiti Mummy" "Na ji muryarka ƙasa-ƙasa wani iri, menene?" "Rahama na yi wa C.S, ta haihu ɗan babu rai". "To kuma shi ne me? Ba zaka raba kanka da harkar mutanen banza nan marasa mutunci da suka ɗaureka ba ko? Ka dawo gida babanka yana hanya zai shigo Kano, yana son ganinka, tun da kai ba ka ga dacewar ka je in da yake ba" "Mummy, ɗa na fa na rasa, an yanka 'yar mutane, haryanzu ba ta farfaɗo ba, kawai na kama hanya na tafi na bar su, anya na yi musu adalci kuwa?" A fusace ta ce "Ni ka ke gaya wa haka Abdul?" "Ki yi haƙuri, ba wai rashin kunya bane ba, ko gaya miki magana ne ba, amma duk fa abin da ya samu rahama ni ne sila, zuwa anjima in sha Allah zan dawo, ina jiran ta farfaɗo ne" Ya katse wayar, yana mamakin son kai irin na iyayensa. Ramma ta farfaɗo daga baccin da take yi, suna ta jera mata sannu, kafin ta amsa ta kalli Nabila ta ce "Anty Nabila ina jaririn ne?" Nabila ta ce "Bari a kirawo Abdul ɗin" Aka kirawo Abdul, ya shigo cikin kulawa yana yi mata sannu. Ta ce "Ina babyn?" Ya zauna a gefen gadon ya ce "Ki na ji rahama, ki yi haƙuri da duk abin da Allah ya hukunta mana, babyn bai zo da rai ba, da alama ya ma kwana biyu da mutuwa a cikinki, sai mu yi haƙuri" "Wayyo Allana, Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yanzu duk wannan wahalar da na sha amma ya mutu" Mama ta ce "Ke ramma, ba musulma ba ce ke? Ba za ki yi tawakalli ba?" "Mama na sha wahala fa, amma ya mutu" ta yi maganar tana kuka. "To dan ubanki sai ki dawo da shi, ke da ki ka samu kanki lafiya ƙalau ba zaki gode wa Allah ba?" Ramma ta kasa jurewa ta fashe da kuka, Abdul ya yi shiru ya ma rasa me zai ce mata, shi kansa kukan yake son yayi, saboda ya saka rai sosai da sosai. "Rahama" Viper ya kira sunanta. "Na'am" ta faɗa tana ɗaga kanta ta kalleshi. Ya ƙarasa gaban gadonta ya ce "Ba a jayayya da ikon Allah kin ji ko? Mamanki da ta rasa Nura haƙuri tayi, nima na rasa ɗa na da matata da tsohon cikin da na ƙallafa rai a kansa, amma ko ganinsa ban yi ba, na rasata na rasa ɗan, dan haka ki yi haƙuri ki yi masa addu'a" Ya nuna mata jaririn nata, ta kai hannu ta taɓa fuskarsa ta ce "Shikenan, Allah ya jiƙansa ya sa ya huta" Abdul ya ce "Amin, ki yi haƙuri kin ji madam, Allah ya kawo mai amfani, ki kwantar da hankalinki, dan a samu ki warke da wuri" ta jinjina masa kai. Viper ya saka yaron a kwali, ya ce wa Abdul, "Mu je a binne shi ko?" Abdul ya jinjina kai, har magariba Nabila na tare da su rahama, ana ta rarrashinta, daga baya tayi musu sallama ta tafi gida. Sai da Viper ya tabattar da su mama basa buƙatar komai, sannan ya tafi. Muktar ya daɗe yana ba wa Abdul labarin Viper da matarsa, da yadda aka liƙa masa kashe matar ta sa, har yake gaya masa yaje kotu ya bayar da shaida a kan shari'ar, tare da nanata Naja'atu Bunkure ba ta da imani. Abdul ya yi shiru yana tunani, tabbas duk abin da Viper yayi, tirsasa masa aka yi, an cutar da shi da yawa, dole ya tsane shi. Jikinsa a sanyaye ya koma gida, yana hasko cewa shi ɗansa kawai ya rasa, duk ya damu ya shiga cikin tashin hankali, amma shi Viper da matar da ɗan ya rasa, kuma aka ɗaure shi aka tauye masa hakkinsa. Da haka ya ƙarasa gida. Yana zuwa gidan ya shiga falon Mummy, suna tare da Indabo, yana cin abincin dare. Ko zama bai yi ba, ta hau shi da faɗa, ta in da ta shiga ba ta nan take fita ba, tana kiransa mara zuciya da bai san ciwon kansa ba. Cikin takaici da mutuwar jiki, ya ce "Mummy ɗa na fa na rasa, haihuwa aka yi mini ɗan ya koma, kuma ɗa na halal ɗan sunna. Mummy idan iyayen rahama sun saka an rufe ni, meye na ɗa na a ciki? Yadda ki ke jin so da ƙaunarmu, haka nake ji a raina, ɗa na ne ya zo babu rai, amma baki tausaya mini ba, baki jajanta mini ba sai faɗa ki ke yi mini ya zan yi ne?" Indabo ya ce "Abdul" Abdul ya kalle shi ya ce "Zo nan" Abdul ya ƙarasa gaban digning ɗin ya ce "Gani" "Zauna mu yi magana" Abdul ya ja kujera ya zauna yana sauraren indabo. "Yanzu Abdul duk abin da ka haddasa, duk bai dameka ba ko? Ka wulaƙantar mini da kuɗi, a kan shashashar 'yar ƙauye, ka yi asarar takarar da nake ta fafutukar na tsayar da kai, dan na san ina tsayar da kai, za ayi caa a tona asirinka, a sake ɓata mana suna, yanzu ni na riga na san na yi asarar takarata duk saboda wawancinka, kuma still baka yi regreting ba, kana faɗar maganganu kana cikin hayyacinka kuwa Abdul? Tun wuri tun da ta haihu, shikenan ina son lallai ka rabu da yarinyar nan, ka fita harkarta, ka zo ayi settling maganarka da yar party chairman haryanzu muna da sauran chances, a next tenure za a iya baka minista, ni kuma in san abin yi. Dan haka lallai ka saketa tun da dama ba wanda ya san ka aureta" Ya kalli mahaufinsa cikin matsanancin takaici ya ce "Daddy, yadda Jafar yake Mexico a tsare, ranka yake maka zafi saboda an tsare maka 'ya, haka maman rahama take ji, koma fiye a duk lokacin da ta tuna na keta wa 'yar ta haddi. Ba dan na zaɓi rahama a kan ku iyayena ba, amma sai da rahama ta shigo rayuwata, na fuskanci gaba ɗaya rayuwata jarrabawa ce, kasancewarku iyayena, babu wanda ya tsawatar mini da shaye-shaye, ko sauran laifuffukan da nake aikatawa ba, kuna kallon hakan a abu ne da zan daina a gaba, rayuwar cikin turawa ya sanya na zama haka. Ban ƙara tabattar da zamanku iyayena jarrabawa ce ba, dai da na nuna maka videon mummunan aikin da ka aikata, amma hakan bai wani dame ka ba, kuma bai girgiza Mummy ba, saboda duniyar ce kawai a gabanku, ni kuwa tuni rahama ta ankarar da ni fifikon Lahirata a kan duniya saboda ita ce dahir. Na miƙa lamurana ga Allah, la'akari da Annabin Allah ma, Annabi Ibrahim alaihi salam, Allah ya jarrabe shi a kan mahaifinsa, haka an jarabci Annabi nuhu da ɗansa, kowane bawa da irin ƙaddararsa, wallahi ku ka ci gaba da matsa mini, zan bar gidan nan, zan je na ci gaba da rayuwata kawai" Indabo ya kwantar da murya ya ce "Haba Abdul, duk wannan abubuwan da kaga ina aikatawa, duk dan mu yi surviving ne, na inganta rayuwarku, kuma abin da ka gani abu ne da ya riga ya wuce, na daina aikatawa, kowane ɗan Adam akwai irin laifin da yake yi wa Allah, kuma Allah mai rahama ne da jin ƙai" "Amma Allah ba abokin wasanmu bane, da dan muna taƙama da mai rahama ne da jin ƙai, zamu din ha aikata zunubai yadda muka ga dama, mu ce gafurun rahimu ne ba. Kuma ace ɗan Adam baya kunyar saɓawa Ubangiji, Daddy har kisan kai fa ka ke saka wa a yi" Indabo ya ce "Wa na ce a kashe?" "Matar Aminu Viper, dan ɗan uwan rahama ne matata, aka kashe matarsa da ɗansa, ita laifin me ta aikata?" "Shi ne yake hure maka kunne kenan? Shiga gonata yayi, na ce aje a koya mass hankali, tsautsayi ya faɗa kan matarsa" Hawaye na bin fuskar Abdul ya ce "Kun samu ssɓani saboda yayi barazanar tona maka asiri na abun da na yi wa yayan rahama, ka tura a kashe shi, aka kashe matarsa, kuma sai aka ɗora masa laifin. Daddy su iyaye ba a canza su, kuma ba a wulaƙanta su, ko da kuwa mushirikai ne, shiyasa tun a wancan lokacin na yi shiru na ci gaba da yi muku biyayya, kamar yadda Annabi Ibrahim alaihi salam yayi. Amma muddin ku ka ci gaba da takura mini, a kan rabuwa da rahama, zan bar gidan nan gaba ɗaya. Allah ne ya tashi kama ni, ya sanya na keta mata haddi ya jarrabe ni da son ta. Allah ne ha so ni da rahama, na haɗu da rahama, kuma shigowarta rayuwata ta zo mini da tarin alkhairi, ni duk abin da suka yi mini, ban ji haushi ba, domin kuwa ma sassauta mini suka yi, dan Allah ku bar ni na ji da zafin da zuciyata take yi mini dan Allah" yayi maganar yana haɗa hannayensa alamar magiya. Har Mummy za ta yi magana, Indabo ya ɗaga mata hannu, Abdul ya wuce yana share hawaye, yana jin zuciyarsa na wani irin zafi saboda tuna wasu abubuwan. ***** Viper ya tafi tare da Abbu ya duba ramma a asibiti. Abbu sun yi hira sosai, dan sai da hirar ta tuna masa da marigayiyya matarsa babbar su Viper zahra'u. Abdul yana ta zarya a kan rahama, baya damuwa da shan ƙamshin da mama take yi masa, hatta medications ɗin ta, shi yake serving. Duk abin da ake buƙata haka yake yi mata, baya nuna gazawa, dama yana zuwa mama ke bar musu ɗakin. Ranar da Abbu ya zo duba ramma, Nabila ma tana nan, yana ankare da su daga ita har Viper, babu wanda yake kula wani, yayi musu shiru bai ce musu komai ba. Sai da Ramma ta kwana biyar a asibiti, sannan Abdul ya yadda a sallameta, babu wani abu da yake damunta, ta samu sauƙi sosai da sosai. Nabila na zaune a ɗakinta, a kan gado, ta baje takardu tana duddubawa tana nazarin shari'oin da take da su. Abba yayi sallama a ɗakinta, ta amsa masa ta miƙe tana faɗin "Abba Allah ya sa ba laifi nayi ba?" "Saboda kin saba da aikata laifuffuka ba" ta ɗan yi murmushi. Ya zauna a gefen gadonsa ya ce "Maganganu ne da ni nake son mu yi" yayi maganar yana kallon jikin wardrobe ɗin ta, duk ta liƙe shi da hoton maciji da stickers na Viper. Ta ce "To Abba ina jinka" "Yanayin alaƙarki da ɗan uwanki Nasir, dan Allah ina son komai ya wuce, ba na son gabar da ku ke yi sam" "Abba ba gaba nake da shi ba, kawai ika mamakin yadda ya din ga kware mini baya ne, yana haɗa ni da kai" Major ya ce "Na sani Arfa, amma Nasir ba ƙashin yarwa bane, kin san kowane ɗan Adam tara yake bai cika goma ba, kuma abin da ya aikata shi ake kira da rauni, irin na ɗan Adam" Nabila ta jinjina kai ta ce "Haka ne" "Yauwwa dan Allah ya wuce ki yi haƙuri" "To Abba, in sha Allah ya wuce, Allah ya yafe mana baki ɗaya, yanzu ka yarda gaskiyar da ka tarbiyyantar da ni a kai a kanta nake dagewa, shiyasa wasu lokutan ake ganina kamar mara ji, ko mara ɗa'a ko" Yayi dariya ya ce "Na yarda, Allah ya ci gaba da dafa miki" Ta amsa da "Amin" "Abu na gaba, babanki ya ce na gaya miki, An tsayar da ranar auren sisternki, ƙarshe watan nan, za a sake ɗaura aure, ta koma gidan tsohon mijinta, Alhaji mu'azzam" Nabila cikin farinciki ta ce "Alhamdilillah ala kulli halin, na ji daɗi sosai da sosai nayi farinciki, Allah ya sanya musu albarka ya daidaita su" ya amsa da "Amin, to ke ya naki batun ne? Kin ce ba kya son yaron nan, babansa sai magiya yake yi yana roƙo, ga Sumayya mamanta ta yi mini magana, wani ya fito ya ce shi kuɗin aure zai kawo, ke kuma kin ja bakinki kin yi shiru, baban yaron nan ya damu lallai a ba wa ɗan sa ke" Jiki a sanyaye Nabila ta ce "Haryanzu Abbu bai haƙura ba? Wallahi ina jin nauyinsa sosai da sosai, amma ba zan iya auren Vi ba" "Meye kuma vi?" "Au Al'amin" "Haryanzu yana shaye-shayen ne da harkar daba?" Ta girgiza kai ta ce "A'a, ai yanzu soja ne, kuma yana zuwa asibitin ƙwaƙwalwa, duk ya rage yin wasu abubuwan, kawai dai ba na son sa ne" "Ita kuma wallpaper ɗinki, da wannan liƙe-liƙen na ɗakinki, duk cikin tsanar ta sa ne?" Cikin jin kunya ta ce "A'a Abba, kawai dai ina sakawa ne, a lokacin ina da hope na ganin na saka kotu ta wanke shi daga zargi" Abba ya tashi ya ce "Gaskiya ne, to ni dai duk hukuncin da babanki ya yanke ba ni da ta cewa, tun da na ga shi ma yana yin yaron, ni na fita sai na dawo" "A dawo lafiya" "Allah ya sa" ***** Rahila ta ɗaga hankalinta sosai, ganin da gaske Walid da ba shi da komai zai aura wa Shahida, babu irin zagin da ba ta yi wa shahida ba, amma tayi bore ta ce ba ta so, amma Shahida ta ce ita ta ji ta gani. Abbu ya ce "Ke dama ban isa sa ke ba, Shahida kuwa 'ya ta ce, dan haka ina da ikon zartar da duk wani hukunci a kan ta, idan bai yi miki ba, zaki iya tattara kayanki ki ƙara gaba, dan albarkacin ta kawai ki ke ci ki ke zaune a gidan nan" haka suka yi faɗa kaca-kaca, ƙarshe Shahida sai komawa tayi cikin ɗaki tana kuka. Da daddare da Viper ya je gidan, ya ga Shahida kamar ba ta walwala, yake tambayarta ko lafiya. Cikin damuwa ta ce "Dan Allah yaya, ka roƙa mini Abbu, na ji ya ce saboda ni mama take zaune a cikin gidan nan, dan Allah ka ba shi haƙuri, na san tun ba yau ba, yana matuƙar haƙuri da ita, amma dan Allah yayi haƙuri, ba ta da cikakkiyar lafiya kuma idan ya rabu da ita, babu in da za ta je, dan Allah yayi haƙuri" Viper ya ce "Kar ki damu, barazana yake yi mata, kin san shi da tausayi, da kuma fushi wasu lokutan, amma in sha Allah ba zai rabu da ita, duk a kan maganar aurenki ne ko?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "Ba zigaki nake ki bijire mata ba, amma ki samu miji irin Walid, sai kin daɗe kina tonawa, tun da ki ka ga Abbu ya amince shi ma, ba mutumin banza bane ba" Shahida ta ce "Haka ne Yaya, ni dan Allah ma ka yi masa magana, wai ba zai yadda a bashi aurena, kuma a bashi wurin zama ba, wai haya zai kama, kuma ya dage sai ya yi mini kayan lefe ko babu yawa. Naga ba ƙarfi ne da shi ba, kuma ni ina duk abin buƙata. Budurwa ce ni ba bazawara ba, amma yaƙi yadda" "Muhsin bai yarda da gazawa ba, wannan wata aƙida ce da muke da ita, ko zamu yi a raina, mun fi son mu ƙoƙarta, amma ki kwantar da hankalinki, zan yi magana da shi in sha Allah, kuma da mun kammala shiri, ba jira zamu tsaya ba da an kawo kuɗin aure lokaci za a tsayar, duk abin da ki ke buƙata ki gaya mini" Shahida ta amsa da "To yaya in sha Allah " Wasa-wasa girma ya hau kan Viper, ɓangaren ramma shi ne, haka gidansu, ga liti ga Walid, kowa Viper. Al'amin sai da ya fara tausayawa Abdul, Abdul bai furta a bashi ramma ba, amma yadda yake sintiri kullum a tafe, ya ƙara tabattar da gaisuwa yake gami da roƙon iri, a kan a bashi matarsa. Ita kanta mama ta ɗan fara saukkowa, ta zuba musu ido. Dan kuwa duk da jaririn ya mutu, sai da ya yanka san da ya saya ya ce idan ta haihu za ayi mata amfani da shi. Duk da kayan da take da su, sai da yayi mata sayayya fal, na kayan sakawa. Ranar da ya kawo, ta din ga yi masa godiya, ya tambayeta, me take so ta karanta zai yi processing komawarta makaranta. "Nurse nake son zama" Yayi murmushi ya ce "Shikenan, sai mu ƙarfafi asibitocinmu, mu kula da su sosai da sosai, amma rahama zaki dawo gidana sai ki yi karatun?" Ramma ta ce "Ai ka san wannan ba maganata ba ce ba, maganar mama ce da yaya Aminu, amma kuma idan na dawo gidanka ai ba zan samu yin karatun ba, an ce ba a ɗaukar masu ciki" Abdul ya ce "No, sai mu yi planing zuwa lokacin da zaki kammala" Ta ce "Anya kuwa, yadda ka ke son yara, kar in je ka canza shawara" "Haba rahama, kin fi kowa sanin halina, ni ɗan Adam ne, amma ban fiye yi wa mutum ƙarya ba dan ya yarda da ni, duk son yarana dolena na jure, kema na ga na inganta rayuwarki na kafa ki" "To ka bari yaya Aminu ya dawo, ya koma wurin aiki ne, amma ka fara yi wa Daddy magana tukuna" "Waye daddyn?" "Alhaji mu'azzam mana, ko da nayi aiki a gidansa, ai haka ake ce masa" "To shikenan, zan yi masa magana in sha Allah, kin san za a mayar da aurensa da yayar Nabila Hafsa". "Ai ban santa ba, ni lokacin anty Jidda na fara aiki a gidan" Abdul ya ce "Ok haka ne, ta koma gida ma, wai sai ya saketa duk a kan case ɗin mu, ni kowa ya ƙarata, a bar mini matata kawai" Tayi murmushi suka cigaba da hira. Nabila sai da tayi ta rarrashin Hafsa, a kan tayi haƙuri ta koma gidan Alhaji mu'azzam, dan fafur cewa tayi ba ta sonsa. Kasancewar duk ƙarshen wata, sai tayi sayayya taje ta gaida Baba, hakan ya saka sun shaƙu sosai da hafsa, sai dai sauran mutanen gidan babu ruwanta da su, idan aka cire saifu, shi ma suna gaisawa. Tare suka ta shirye-shirye, Hafsa tana cewa ita babu wani gyara da zata yi, lokacin da aka yi na farin ma, bai yi mata amfani ba balle yanzu. Amma Nabila da taimakon sumayya suka ce, sai ta yi gyara da da yanzu ba ɗaya bane ba, zamani ya riga ya canza. A lokacin Shahida ma Walid ya kai kuɗin aure, kuma Hafsa ƙawar Shahida ce, kasancewar iyayensu aminai ne. Watanni biyar aka saka, saboda babu yadda Viper bai yi da Walid ba, ya dage ya ce shi sai yayi mata lefe ko yaya yake, kuma sai ya kama gida. Shi ba ruwansa da bazawara ce, ba zai so ace shi aurensa na fari, ace ya naɗe hannu komai sai dai ayi masa ba. Viper ya ce masa ya gyara nasa gidan, su zauna sai ya din ga biyansa kuɗin hayar. Walid ya ce "Ai sakankancewa zan yi, na san naka ne, idan ma ban biya hayar ba, ba zaka damu ba, kuma zan ta damuwa gidan zai din ga tuna mini ƙanwata Jauhar, kuma kai a ina zaka zauna, idan ka yi naka auren?" Viper ya ce "Ina da wurin zama ai ni, ko ka ƙi, ina wani gidan, na ji ba zan saka maka hannu ba, ka gyara shi da kanka, kayi lefen, amma ba zaka kama haya ba gaskiya ba" Da kyar Walid ya amince da hakan, sai dai Liti ya zage kamar kayan lefensa zai tara, kuma Nabila suke turawa kuɗi take haɗa kayan, ita kanta Shahidan ba ta san da haka ba" Sai dai daga Hafsa har Shahida sun dawo daga rakiyar iyayensu, na shirmen bin bokaye, domin sun tabattar da ba hanya ce mai ɓullewa ba. Kasancewar Sumayya na ta'amalli da mutane daban-daban, a dalilin harkar aikinta, ya sanya ta nemi lambar maman dr., Domin haɗawa Alhaji mu'azzam da kuma ango Walid amayarsa. Tun da ita mace duk in da take sai da gyara. Kuma masu iya magana suka ce, idan kana da kyau ka ƙara wanka. A cikin wata gudan nan, ba ƙaramin kyau Hafsat tayi ba, sai sheƙi tayi gwanin sha'awa, duk da ba ta da jiki, amma maman dr. Ta tsatsota, ta cika tayi fam, tayi ƙiba dai-dai misali, amma duk lokacin da Alhaji mu'zzam ya zo sai sun yi faɗa. Gashi can gidansa uwargidansa ta sako shi a gaba a kan ya ce zai dawo da hafsa, rashin mutunci na yau daban na gobe daban, gaba ɗaya ta ƙaurace masa, yadda Jidda ma ta fita, so take ta rayu itakaɗai a gidanta, shi kuma ya ce bata isa ba, yana da wadata da lafiyar da zai auri mace fiye da ɗaya. Ya din ga ganin tamkar ranaku ba sa sauri, duk lokacin da ya je wurinta, da kyar yake saita nutsuwarsa, saboda kyan da tayi, da wani irin sihirtaccen ƙamshi da take yi. (Domin gyara da kankaro naku mutuncin kuma a naku gidajen auren, ku garzaya ku tuntuɓi maman dr. Likktar mata domin kar ayi babu ku 07069711327) Viper yana zaune yana duba status ɗin sa na waya, yana son ya halarci ɗaurin auren hafsa, dan haka yana saka ran ana idar da sallar asuba zai nufo Kano, duk da ɗaurin auren na azahar ne sai an saukko daga masallaci. Status ɗin Nabila da ya yi muting ya shiga, na farko Addu'a ce, kamar yadda ya zame mata ɗabi'a, yawan sanya addu'oi da shot videos na malamai. Na gaba kuma, videonta ne, an yi mata lalle ja da baƙi, sumayya tana cewa our dear barrister marasa galihu, jin ki yafi ganinki, our anti serious beb" ta kwaɓe fuska tana harar Sumayya. Ɗaya Videon kuma, Ita da sumayya ne da amarya hafsa, da wasu daga cikin yayyen su mata. Haushi ne ya kama shi, ya san wataƙila duk mazan da suke cikin wayarta sun ga status ɗin, doguwar riga ce a jikinta, ta ɗora mayafinta a kanta, shigarta decent amma shi abin da idonsa yake gani, gani yake kowama ya gani. A irin fitinarta, duk abin da Hafsa take amfani da shi na gyara, sai ta ce sai ta sammata. Nabila kuwa tana saurar tashar su Sumayya, At the same time tana chatting, Sumayya na shirye-shiryen rufe tashar, ta fara sanar da ɗaurin auren hafsa, sannan ta ambaci na Nabila da Al'amin, a babban masallacin juma'a na BUK wanda za a ɗaura bayan an idar da sallar juma'a. Ayshercool 08081012143 105 Miƙewa Nabila ta yi tsaye, tana tunanin kamar ba ta ji sosai ba. "Wane irin wasan banza ne haka sumayya take yi mini?" Tayi maganar tana mamaki. Wayar Sumayyan ta hau kira, amma wayarta a kashe, jikinta na rawa ta fito falo, amma ta tarar kowa ya kwanta, ko ina a rufe. Ta koma ta hau kiran Umman Sumayya, amma ita ma ta ta wayar a kashe. Ta saka wa zuciyarta zolaya ce kawai Sumayya take yi mata, dan tun da aka yi musu lallae take cewa tayi kyau kamar ranar tarewa a gidan Viper. Sai dai wannan ya wuce wasa, ta rasa meyakamata tayi, ta din ga fatan Allah ya sa mafarki ne ba gaske ba. Gaba ɗaya ta kasa bacci, sai dai yadda ta kasa baccin nan, haka Nasir ya kasa, da yayi juyi ya kalli invitation ɗin auren Nabila, sai gabansa yayi wata irin mummunar faɗuwa, cike da baƙin ciki da damuwa. Ya so Nabila tun tana 'yar ƙarama, tun tana yawo ba riga, ba ta san ciwon kanta ba, yana matuƙar tausayinta, yana taya major ƙaunarta, saboda maraicinta, ga rashin lafiya ga kuma ƙiyayyar da mutanen gida suke yi mata. Wahalarta babu wadda bai sha ba, kaita makaranta, yawon visiting kaita Asibiti idan Major baya nan, duk wata gudunmawa da ya san zai iya bayarwa domin ta ji daɗi yana yin su. Duk rashin jin ta da karaɗinta baya damunsa, babban burnsa ya ganta tana cikin faranciki, mussaman idan yayi la'akari da hadisan Annabi Sallallahu alaihi Wasallam, da suka yi magana a kan kula da maraya, idan ya tuna mamanta ta rasu, ba ta san waye babanta ba, sai matsanancin tausayinsa ya ƙara shigarta. Bayan Major ba ta da wasu da yadda da su take ƙaunar su, sama da shi da Sumayya, koma Yaya Nasir ko Sumayya, duk wata wauta da taɓara da zata yi, baya gajiya, da hakan matsanancin son ta ya shiga ransa, sai dai mama ta riga tayi masa kandagarki da Allah ya isa a kan Nabila, tsawon lokacin nan baya iya kula kowacce mace, saboda Nabila, sai dai duk wannan son da yake yi mata, lokaci ɗaya kuɗi suka rufe masa ido, ya tafka mummunan kuskuren da ya rushe waccan kyakkyawar alaƙar da take tsakaninsu, har ta kai tana yi masa kallon maƙiyinta a yanzu. Da Asuba Viper ya nufo Kano, Abbu ya kira shi a waya, suka gaisa ya ce "Ka taho ɗin ne, zaka halarci ɗaurin auren?" "Eh in sha Allah Abbu, ai ina hanya ma, na biyo sojoji mun taho" "Akwai kuɗi a wurinka ne?" Viper ya ce "Eh, amma kamar nawa?" Abbu ya ce "Dubu ɗari biyu" "Eh ba za a rasa ba" "To da ka dawo ka taho gida da kuɗin, ina son ganinka" "To in sha Allah, ina nan tafe" "Allah ya kawo mini kai lafiya" Viper ya yi murmushi ya ajiye wayar. Sai dai babu daɗewa Walid ma ya kira shi, ya ɗaga ya ce "Mazaje ya ne?" Walid ya ce "Mai zamani" "Mai laya?" "Za ka zo ɗaurin auren yayar Nabila ne?" "Eh in sha Allah" Walid ya ce "To ka yi sauri" "Me zaka bani, ba sai bayan juma'a ne ɗaurin auren ba?" "Eh kawai dai ka yi sauri" Viper ya ce "To aiko mini da fuka-fukai na tashi sama" Walid ya yi dariya ya ce "To in dai zaka yi sauri ai shikenan" ***** Wayewar garin Allah, Ana idar da sallar asuba, Nabila ta tafi ɗakin Abba, ta tarar bai ma dawo daga masallaci ba, ta samu wuri ta zauna tana jiran dawowarsa. Yana yin sallama ta tashi tsaye, ta ce "Abba, ina kwana?" "Lafiya ƙalau, kin tashi lafiya?" "Abba ni fa ban yi bacci ba, Sumayya ce ta yi mini wani wasan banza da ya ɗaga mini hankali, wallahi ido biyu na kwana cikin zullumi da fargaba, na zata mafarki ne ma zan farka, amma dai na ga gaske ne" Ya zauna yana faɗin "Subhanallah, wane irin wasa ne haka, da ya hana barrister bacci?" "Ɗaurin auren hafsa ta sanar, kuma sai na ji ta faɗi sunana da na Viper, wai za a ɗaura mana aure" Major ya ce "Ikon Allah, kuma kin kira wayarta?" Ta ce "N kirata wayar a kashe, na kira ta Umma ma, amma ba ta shiga duka" Abba ya jinjina kai ya ce "Abin da mamaki gaskiya, bai kamata ta yi miki wannan wasan ba gaskiya, amma ki je ki samu ki yi bacci, na san da wasa take yi miki, wurin ƙarfe goma sai ki shirya ki tafi can gidan naku wurin bikin, na ji Antynki da su Magajiya duk suma za su je" Ta ce "To Abba" sai ta ji ƙwarin gwiwa, ta je ta nemi wuri ta kwanta, sai ta samu bacci ya ɗauke ta. Tana farkawa, Sumayya ta fara kira, wayar ta shiga amma Sumayya taƙi ɗagawa, hakan ya ƙara fusata ta. Ta fita kitchen, tana gaya wa baba magajiya abin da tayi mata cike da takaici. Baba magajiya ta ce "Kun fi kusa, ina fatan Allah ya tabattar mana da alkhairi" "Ba amin ba, ba da shi ba alkhairin" Baba magajiya ta ce "Au zaki ga ba da shi ba, ni dai ina yin sa, duk da ya ce kar na gaya miki, ranar da suka zo, dubu goma ya bani, ya ce na sha lemo, a samarinki waye ya taɓa saurarata" A shagwaɓe ta ce "Ni fa ba saurayina ba ne ba" "Oho miki dai, ni dai Allah ya zaɓa abin da ya fi alkhairi" Nabila ba ta sake cewa komai ba, ta hau bubbuɗe kwanuka, ta buɗe fridge ta ɗauki gasarar alkama, ta dama kunu da ita, ta ɗebi doya ta dafa ta ɗebi miya ta koma ɗaki. Ta fara karyawa, ta shiga facebook, saboda tana buɗe data, notifications suka din ga shigowa ba ƙaƙƙautawa. Ai tana shiga da invitation ɗin ta fara cin karo, ana ta yi mata Allah ya sanya alkhairi, ba ta san lokacin da ture kofin kunun ba, ta tashi da sauri, har tana tuntuɓe, ta shiga ɗakin major tana zazzare ido. Ta tarar da shi tare da telansa, ta ce "Abba ka ga fa" tayi maganar tana haska masa fuskar wayarta. Ya sallami telan sannan ya ce "Zauna mu yi magana" Ta zauna jikinta yana tsumar rashin sanin abin yi. "Nabilatul arfa, tun da mahaifiyarki ta rasu ta bar mini ke, nake kula da ke cikin ikon Allah, tamkar ita nake kallo, ban taɓa yi miki wani abu da zai cutar da ratuwarki ba. Kuma na daɗe ina baki dama na aikata duk abin da ki ke so, muddin ba gani nayi zai cutar da ke ba, babu irin ƙalubale da bamu fuskanta ba daga ni har ke, amma na toshe kunnuwana, domin ganin kin rayu cikin farin ciki da jin daɗi. Wannan hukuncin mahaifinki ne ya yanke shi, duk yadda na kai ga nuna miki so da ƙauna, ya fi ni iko da ke, ko da a gaban shari'a ne, na ce ya bani dama na tattauna da ke a kan yaron nan, ya bani amma ki ka nuna ke fafur ba kya son sa. Kafin na amince da maganar Al'amin, na yi bincike a kansa fiye da yadda ki ke tunani, wurin aikinsa, wurin mahaifinsa, duk wani motsi na rashin jin sa sai da aka bani labari. Na zauna da abokansa, sun bani labarin yadda ki ka shiga rayuwar sa, da duk abin da ki ka din ga yi, rayuwarsa da yar uwakki, wanda shi kansa bai sani ba. Irin rayuwar da ya yi da 'yar uwakki, duk na bincika, gefe guda babansa na ta bi na yana yi mini magiyar a shawo kanki, Allah ma'aiki kar ya koma rayuwarsa ta baya. Honorable Mu'azzam Wada kankarofi, shi ma bai ɓoye mini komai ba, shi ya ƙara ƙarfafa lallai ayi auren nan, zaku zauna yana sonki kina sonsa, ke kuma naga gaba ɗaya shirme ne a kanki da wauta, dan haka muka yanke wannan hukunci. Sumayya ba wasa ta faɗa ba, katin aurenki ne, kuma ina fatan zaki yi mana biyayya baki ɗaya" Ƙurawa Abba ido ta yi, ji take kamar almara, kawai kuma ta fashe da kuka "Abba ka fa ce ba zaka yi mini auren dole ba, haba Abba" "Wannan ai ba na dolen bane ba" "Haba Abba, na dole ne mana, ba sai an tambayi mutum yana so ko ba ya so ba, kuma ka tambayeni na ce a'a kawai kuma sai a ɗaura" Ya ce "Eh gaskiya ne, ban kyauta ba, za'a kai ƙarata kenan, na taɓa masu shari'a" Yanayin yadda yayi maganar ya sanya ta gane zolayarta ma yake yi, bai ɗauki hakan serious ba. Hakan ya saka ta ƙara sautin kukanta har da sheshsheƙa. Abba ya ce "Maza yi ta yi, in dai kukan banza ne, dama tun kina zanin goyo halinki ne, idan ki ka isheni kuma, na zane miki jikinki" "Abba ba na son shi fa, gaba ɗaya baya so na, ai an baka labarinsa da Jauhar, ya ce duk duniya itakaɗai ce mace, ba fa ya so na ko kaɗan, Wannan auren dole ne Abba" "To Arfa a kaini gaban me Shari'a a tuhume ni da laifin child abuse, na yi wa barrister auren dole, amma sai ki haɗa da ni da ubanki duk ki kaimu ƙara. Kai waye a nan wurin ku kira mini magajiya ta zo ta ɗauki yarinyar nan daga gabana, kafin na casata a wurin nan" Ƙarshe ya tashi ya bar ta a wurin, tana ta gursheƙen kuka, kamar an sanar da ita mutuwar tsohuwarta. **** Ƙarfe sha ɗaya Viper ya shiga gida, Abbu ya ce "Dama tuntuni kai nake jira, ka ƙaraso mu karya" Viper ya yi murmushi, yana jin daɗin tattalin nan da Abbun yake yi masa. Ya ce "Abbu ya su Walid kuma?" Abbu ya ce "Yaran kirki, Abdallah babansa ya kai shi kasuwa, wurin sayar da sarƙoƙi da kayan shafe-shafen mata, ya ce a kama masa shago, idan ya gane kan harkar sosai, yaƙi zama muna tare da shi a kasuwarmu, wai shi ba ɗan daudu ba, me zai yi da wani kayan shafe-shafen mata. Na daɗe ban ga rigimammen mutum kamarsa ba, yanzu haka ma suna kasuwa ne kayanmu zasu iso, daga nan za su yi mini wani aiki, da yanzu ka gansu a nan. Na je gida mun yi magana da mahaifinsa na ce yayi haƙuri ya ƙyale shi, tun da ga in da hankalinsa ya karkata". Viper ya ce "Liti akwai rigima, wanda bai san halinsa ba ba zai iya zama da shi ba" Abbu ya ce "Ai naga alama, akwai barkwanci" "Idan yana yin mutum kena ba, amma ga wanda bai san shi ba, goga ne, a lokacin muna mazaje, muna ji da rashin ji, ya fi Walid karsashi, 'yan daba idan sun kai goma, zai ratsasu shikaɗai ba ya tsoro ba kuma ya san wargi" Abbu ya rausayar da kai ya ce "Na so ace tuntuni na farga, na ja ku a jiki ku duka, da kai ɗin da su, na riƙe ku na kula da iliminku, na kaiku kasuwa, da yanzu Allah kaɗai ya san me zaku zama, su waɗanda nake kallon su ne shiryayyun na ɗauki ɗawainiyar su, gashi a ƙarshe ba wanda ya more su, na yarda da ɗa da dukiya ba a yi musu mugunta, yanzu gashi ku ɗin da ake kallon marasa ji, yanzu al'umma sun fara amfanar ku, ba zan manta da honorable wada kankarofi ba, bawan Allahn nan ɗan halak ne, gashi ka zama soja kana aikinka, Allah ya ƙara dafa muku" Viper ya ce "Amin" Abbu ya ce "Amma ya aka yi ka ke da kuɗi tsakiyar wata, ai ni da na ce ka taho da 200k da idan ka ce babu, zan ƙara nuna maka amfanin haɗa kasuwanci da aiki ne, an ce albashin naku, ba shi da yawa". Viper ya yi wata irin dariya ya ce "Ko a cikin sojoji, irin aikinmu na musamman ne, kuma mai hatsarin gaske, ina da salary mai kyau, zan zaɓi garin da nake so a bani gida, kuma za a bani abin hawa, ba a buƙatar rashin gskiya ko a samu irinmu da halin cin amanar ƙasa, idan aka kama mu da haka, babu shari'a kisan kai ne kawai. Shiyasa irinmu a sojoji ba su da yawa ko kaɗan" Cikin mamaki Abbu ya ce "Wai bayan fitowar ka har ka yi training ɗin ko kuwa? Kuma wane iri ne aikin naku a sojoji?" "Ina gaya maka kashe ni za ayi, ba a faɗa kawai dai ka saka a zuciyarka ɗanka soja ne, mai muhimmancin gaske ga ƙasarsa, kuma a kowane lokaci zaka iya rasa shi, dan haka ka yi mini addu'a kawai" Abbu ya ce "In sha Allah sai ka yi retire da kanka daga aiki, ba za a kashe ka ba" haka Abbu ya din ga jan sa da hira, har lokacin salla ya ƙarato. Abbu ya ɗaukko masa sababin kayan kar, dark blue ɗin shadda, riga da wando, da hula. Ga sabon agogo da takalmi. Ya ce "Wannan fa?" Abbu ya ce "Wurin ɗaurin aure zamu je, ba na son yawon da ku ke yi da ƙanan kayan nan, kamar ba yaran hausawa ba, dan haka su zaka saka" Shafa kayan ya yi, yana tuna abar ƙaunarsa, Jauhar, a lokacin da ta bashi kyautar kaya ranar sallar idin ƙaramar salla. Su Walid ne suka yi sallama a waje, Abbu ya ce ace su shigo, suka shigo sanye da fararen kaya, liti ya riƙo hularsa a hannu. Abbu ya ce "Abdallah, ya ka cire hular ka ga yadda ka yi kyau a cikin kayan kuwa?" Ya ce "Abbu, hular ce ta ɗame mini ƙeya nake ta gumi shi ne na cire" "Ai fa rashin sabo ne" "Mai zamani, Abbu ne fa ya ɗinka mana kaya" liti yayi maganar yana nuna masa kayan jikinsa. Walid ya ce "Mai zamani haka ka ke kyakykyawa, rabon da ka yi kyau kamar haka, tun ranar aurenka da marigayyiya" Abbu ya gyarawa Walid zaman tasa hular, ya ce "Yauwwa ko ku fa 'yan samari, Allah ya nuna mini aurenku duka" suka kasa cewa Amin. Wani farinciki ne ya mamaye zuciyar Viper, ganin yadda Abbu yake nuna wa su Liti ƙauna, wanda ya san duk dan saboda shi ne, shi yanzu a duniya abin da zaka yi masa, ka saka shi farinciki, ka so mutanen nan uku kamar yadda yake ƙaunar su, ya san a duniya ba shi da abin biyansu. Haka suka ɗinguma a mota, suka tafi masallaci, domin yin salla da halartar ɗaurin Alhaji mu'azzam. A sahu ɗaya suka yi salla da Alhaji mu'zzam, suna ta yi masa Allah ya sanya alkhairi. Bayan an idar da salla, babban abin da ya ba wa Viper mamaki, bai wuce ganin abokan Abbu da yawa a wurin ba, da kuma wasu daga cikin 'yan uwansa, bai kawo komai a ransa ba, suka gaggaisa, suna taya shi murnar wanke shi da kotu tayi, wasu kuma na zuzuta kyan da yayi, wasu kuma suna yi masa Allah ya sanya alkhairi, shi dai duk bai gane kan abin ba, ana ta ɗaura aure, aka zo kan na Alhaji mu'azzam, aka ɗaura aurensa da Hafsa. Bayan an kammala na su, aka nemi waliyayyan Al'amin, saroro yayi yana kallonsu, ganin Baba yana kallonsa yana murmushi, haka Major. Ya waiwaya, har da su doctor Muktar, da Abdul yasar a wurin. Sai da aka ɗaura aurensa da Nabila, sannan ya fuskanci abin da yake faruwa. Walid ya cire hular Viper, ya shafa kansa ya ce "Angon Nabila ka sha ƙamshi, yau dai Allah ya yi Allah ya sanya alkhairi" Yayi saroro yana kallonsu, liti ya ce "Mun iya Suprise ko? Sai ka bamu tukuci yasin, idan ka cire kayan nan ni zaka bawa, in saka ranar auren Walidi, ko Allah ya sakani a damshinku" "Mai laya yaushe aka shirya wannan abin, ita Nabilan ta amince ne?" Liti ya ce "Oho muku, mu dai an haɗa kai da mu, an ƙulla sunnar ma'aiki, ai yanzu rumfar shayi har da banner dalilin aure zan saka. Idan aka biye muku, wahalar da mu kawai zaku yi ta yi, yanzu sai ku ƙarata ku sasanta kanku" Aka fito daga masallaci, Viper sai jin sa yake tamkar ba shi ba, abin kamar almara. Alhaji mu'azzam ya ƙarasa ya miƙa wa Viper hannu ya ce "Na haƙura na janye, na kuma yarda Jauhar taka ce, Nabila ma taka ce, ba a takara da kai Viper, duk da ka fuskanci ƙalubalen rayuwa da yawa, amma ina da yaƙinin Allah yana sonka, yadda yake tafiyar da lamuran rayuwarka. Ina yi maka fatan alkhairi, Allah ya baku zaman lafiya mai ɗorewa" Viper ya riƙe hannun Alhaji mu'azzam, amma ya kasa magana sam. Major ma zagayo wa yayi, ya dafa kafaɗar Viper, ya ce "Yadda na samu labarin ka riƙe Jauhar amana, dan Allah ga 'yar uwatta nan ma, Allah shi ya san dalilin da ya sanya ya karɓi jauhar a lokacin da ka ke matsanancin son ta, ya musanya maka da 'yar uwatta, wataƙila da bai ɗauke Jauhar ba, babu yadda za ayi Nabila ta ga mahaifinta, komai sila ne, kuma duk abin da Allah ya yi dai-dai ne, ba a tambayarsa dan me? Allah ya baku zaman lafiya" Viper ya risunar da kai ya ce "In sha Allah Abba, na gode sosai" Abbu ma ƙarasowa yayi, ya ce "Al'amin, a karo na biyu na sake nema maka auren 'ya, kuma Alhaji Bashir ya sake bamu, a rana mai kamar irin ta yau aka ɗaura maka aure da jauhar, yau ba ta raye, an sake ɗaura maka aure da Nabila, dan Allah Al'amin ka riƙe musu 'ya da mutunci da amana" Kawai ya fara zubar da hawaye, duk da yayi iya ƙoƙarin sa wurin mayar da hawayen, amma abu ya gagara, kawai ya lumshe idanunsa ya basu damar su zuba. Major ne ya ce "Ya haka kuma? Amare ke kuka ba angwaye ba, dan Allah kar ka bayar da mazaje mana, soja ne fa kai". Jiki a sanyaye Walid ya ce "Ai a duk lokacin da za ayi wani abu da zai tuna masa da Jauhar duk taurin zuciyar sa da ƙarfin halinsa sai ya yi kuka, haryanzu ya kasa jurewa, duk yadda za a bayar da labarin yadda suka rayu, idan ba wanda ya gani ba ba zai gane ba" Major ya ja shi ya bashi handkerchief ɗin sa, yana duddukan kafaɗarsa yana rarrashinsa, Abbu ya ce "Al'amin dole fa ka yi haƙuri, kayi haƙuri, duk lokacin da ka tuna Jauhar ka yi mata addu'a. Sannan dole ka koyi danne zuciyarka, idan ba haka ba, zaka iya sanya wa Nabila kishin 'yar uwatta, zuciya ba ta da ƙashi". Kallonsu kawai yake yi, idan ya ce ba ya murna da farincikin wannan auren, ƙarya yake yi, amma zuciyarsa ta tsinke, da yaga yana sake ɗaura wani auren, Jauhar ɗin sa ba ta duniya, a lokacin da yake tare da ita, gani yake duk wani leƙe-leƙe da ake faɗa na namiji a kan mace, itakaɗai ta ishe shi rayuwa. Suka kewaye shi suna ta rarrashin sa, abin da ya ƙara yi masa daɗi da sanya shi farinciki, bai wuce yadda shi da ake ƙyama a da, amma aka tara wannan mutanen saboda shi, kuma duk suka kewaye shi, kowa yana ƙoƙarin rarashin sa, lallai babu abin da ya fi zama mutum na gari. Alhaji mu'azzam ya ce "Ko sai mun dangana da wurin amaryar za ta rarrashe shi? Dan naga tafi kowa iya shawo kansa" Major ya ce "A'a bar amaryar nan, ka san ba ta san da bikin ba sai jiya da sumayya ta sanar da daddare, can na baro ta a falo tana kuka, fushi ma take da ni, ina ga ranar Litinin za a kawo mini sammaci daga kotu, na taɓa masu ƙasa na yi wa barrister auren dole, amma na gaya mata ni da kai zata kama, tun da tare muka yi laifin" yayi maganar yana nuna Alhaji Bashir . Suka yi dariya baki ɗaya. Duk da a ƙurarren lokaci Sumayya ta sanar da ɗaurin auren Nabila, Auren ya samu hakarta ɗaruruwan jama'a, manya da ƙananan mutane, mussaman waɗanda suke supporting ayyukanta, har da wakilai daga gidan gwamnati, manyan lauyoyi da baristoci, har da kwamishinan shari'a, da alƙalin alƙalai na jiha. Da yawa saura kwana biyu uku suka samu invitation ɗin, kuma an halarta sosai da sosai. Ba ƙaramin daɗ Major ya ji ba, ganin irin jama'ar da Nabila ta tara, a ransa yayi mata addu'a Allah ya sa yadda ta riƙe gaskiya a kan aikinta, da ta tara wannan jama'ar, Allah ya sa ranar mutuwarta ta tara fiye da haka. Shi kansa Babanta ya yi farinciki, mussman yadda ake ta yabonta, da jinjinawa yadda ta zamo matashiyar yarinya, mara tsoro da jajircewa a aiki. Nabila kuwa har Abba ya tashi ya shiga bedroom ɗin sa, yayi wankansa ya shirya tafiya ɗaurin aure, tana bayan kujera a zaune tana kuka. Gaba ɗaya shi dariya ma take bashi, dan haryanzu kallon yarinya ƙarama sosai yake yi wa Nabila. Baba magajiya ta je tana rangaɗa mata guɗa a ka, amma tana guɗa Nabila ranta na ƙara ɓaci, baba magajiya har da rawa, da yi mata waƙoƙin amare irin na da. Nabila ta koma ɗakinta, sai ga kiran Sumayya, ta ɗaga wayar, Sumayya ta kwashe da dariya tana amarya ba kya laifi. "Da ke aka haɗa baki aka yi mini haka ko Sumayya, ki je kanki ki ka yi wa" Sumayya dariya har da tuntsurawa ta san a rina, rigima da daru, za a sha su akan abin da aka yi wa Nabila. **** Maman ramma kuwa ta tattara ramma da Abdul ta saka musu ido, dan ta fara jin nauyin sa, irin yadda yake hidima da rammar, a da tayi zaton ƙoƙarin sayeta yake son yi da abin duniya, amma sai taga ba haka ba, zunzurutun soyayyar kawai yake yi wa ramman. Yau daga wurin ɗaurin auren Viper, gidansu ramman ya wuce. Tsayawa ramma tayi tana ƙare masa kallo ta ce "Ka ga yadda ka yi kyau kuwa?" "Daga wurin ɗaurin auren yayanki nake" Ramma ta ce "Haka mama take gaya mini, ai shekaranjiya babansa ya zo, ya daɗe a gidan nan suna hira da mama, yake gaya mata halin da ake ciki, yau za a ɗaura musu aure, amma daga ita har shi ba wanda ya sani, na ce ikon Allah kamar film" "Wallahi rahama ya bani tausayi, kin san duk wannan muzuran da yake yi, da shan ƙamshi, amma ya din ga kuka a wurin ɗaurin auren nan, kamar yaro ƙarami, wai ashe wadda ta rasun ya tuna, wallahi sai da na yi masa kuka, muktar ya ce mini duk yadda nake sonki, da nuna miki kulawa, ba zai kai kwatantkwacin son da yake yi mata ba, da na tuna mahaifina ne sila, wallahi sai na rasa in da zan saka raina. Ya ma yi ƙoƙari yake ɗan iya kula ni a 'yan kwanakin nan, dan hau har gaisawa muka yi" Ramma ta ce "Yaya zamu yi, ai ƙaddara ta rigayi fata sai addu'a" Sai da aka yi sati guda, sannan Alhaji mu'azzam tare da hafsa suka ɗaga zuwa babban birnin tarayya Abuja. Gidan Hafsat na Abuja mai kyawun gaske, ya fi wanda ta zauna da ita da uwargidansa a can Kano, sai dai taƙi sakin jiki da shi. Jirgin yamma suka bi, gefin magariba suka sauka. Da ya ɗan matsa kusa da ita, sai ta maze ta matsa tana haɗe rai, dan haka ya rabu da ita. Da daddare da kyar ta yadda ta ci abinci, shi ma ba da yawa ba. Ya riƙo hannunta zata ƙwace, ya riƙe gam, ya ce "Haba hafsatuna, ni ne fa, ki yi haƙuri dan Allah, ki bani dama na gyara kuskuren da nayi miki a baya, Please" tayi shiru, ba ta ce masa komai ba, saboda ta kasa manta mummunan halin da ta faɗa a wancan karon a dalilin aurensa. Da kyar ya lallaɓata, kamar budurwar da ba ta san komai ba, sai dai a wannan karon ita kanta ta san da banbanci, dan a wacan karon, banda tsabar kayan tsubbu, da abubuwan da ba ta san ko na menene ba, da su aka yi mata gyaran jikinta. A wannan karon kuwa, ta san da banbanci, domin kuwa maman dr. Ta kankarota ta kankaro martabarta a idon mijinta, dan a wancan karon ko maganin sanyi ba ta yi amfani da shi ba, sai kayan tsubbu da abubuwan da ƙawaye suka din ga ba ta shawara a kai. Shi kansa yadda ya yi appreciating ɗin ta a wannan karon, ya sha bamban da lokacin da tana budurwa. (07069711327 ga masu buƙatar kayanta, su na iya tuntuɓarta kai tsaye, she's always available for you) ***** Viper kuwa kimanin sati biyu kenan, tun da Allah ya sa aka ɗaura aurensa da Nabil, babu wanda ya nemi wani daga shi har ita, kuma hakan ya ɓatawa kowannensu rai. Abba ya sanar mata, da babu ita babu yawo, idan ba wurin aiki ba, dole sai da izinin Al'amin. Rashin kiranta da bai yi a waya ba, ya tabbatar mata da sam ba ya ƙaunarta, auren dolen ne dai kawai, shi ma ya nemi ya aureta ne kawai saboda mafitarsa. Kasancewar hidimar bikinsa, tare da na Walid za a haɗa, ya sanya yayi delay na komawa aiki, domin sanin shirye-shirye da yakamata yayi. Yana son ya tambayeta, abin da take buƙata na harkar biki, amma ya shareta. Ta koma wurin aikinta, ana ta yi mata Allah ya sanya alkhairi, aka din ga tambayarta meyasa ba ta tafi hutu ba, ta ce ɗaurin aure aka yi, ba ayi biki ba. Aka din ga bata gudunmuwar biki, ta in da ta zata, da in da ba ta ma zata ba. Kawai tana zaune a office taga alert ɗin dubu ɗari biyar, da sunan Al'amin da komai. Sai a lokacin ta kira wayarsa, ya ɗaga amma yayi shiru. "Naga ka turo mini kuɗi" "Ki fara sayen abin da ki ke buƙata na lefe, zan sake turo wasu, na san wannan ba za su isa ba". "Ni bana so" ta faɗa a daƙile. "Menene ba kya son?" "Kuɗin, ni ka bani account number na dawo maka da su" Wani malolon takaici ya ƙule masa zuciya ya ce "Bani da lokacinki, ki same ni a gidan su rahama, sai ki dawo mini da kuɗin" ya kashe wayarsa. Ba tare da tunanin komai ba, ta miƙe ta fara harhaɗa kayanta. Da ta isa gidan su ramam, Maman ramma ta ce "Amarya ke da kanki, ina ta cewa Aminun ya zo ya kai ni gidanku, amma haryanzu shiru" Nabila ta ce "Dama baya nan? cewa fa yayi na zo na same shi a nan" "A'a ya dai ce zai zo, amma bai ƙaraso ba tukuna" yanayin fuskar Nabila da ta gani babu fara'a, ya sanya ta din ga yi mata nasiha, tayi haƙuri ta rungumi mijinta su zauna lafiya kamar yadda yar uwatta tayi. Ita kuwa Nabila gani take, ba zasu gane ba, ba su san waye Al'amin bane. Ita a tata wautar, da gaske zuwa ta yi ta mayar masa da kuɗinsa, sam bai iya rarrashi ba, ba ta san tarko ya yi mata ba. Awanta guda a gidan, ya zo, kuma yaƙi shigowa cikin falon, ya ce ta je ta same shi a sitting room ɗin harabar gidan. Ta tashi ta ce "Mama ina zuwa" ta fita ta ƙarasa ɗakin. Sai dai tana arba da shi, duk wannan fitsarar da take ji da ita, ta nemeta ta rasa, sai tsoro da fargaba da suka mamayeta. Lallai miji yafi gaban wasa. Ya ɗago ya kalleta, doguwar riga ce a jikinta, sai mayafin rigar. Gaba ɗaya Nabila ba ta da wayo, ko kaɗan, abin da ba ta sani ba, ba wai dawo masa da kuɗi ne ya kawota ba, son ganinsa ne ya kawo ta, ba tare da ta yi lissafin hakan ba. Ya kawar da kansa ya ci gaba da danna wayarsa. "Ka bani account number ɗinka, na mayar maka da kuɗinka, ni bana buƙatar komai daga wurnka, ba zaka taɓa iya bani abin da nake so ba". Ramma ta yi sallama da ƙaton faranti, shaƙe da kayan abinci, ta gaida Al'amin ya amsa, ta kalli Nabila da ke tsaye ta haɗe rai, ba ta ce komai ba ta fita. Ta fara ƙosawa da tsayuwar da take yi, ya miƙa mata hannunsa, ba tare da ya Kalle ta ba ya ce, "Bani wayarki na saka miki account number ki dawo mini da kuɗina" babu musu ta ƙarasa ta miƙa wayar, ya yi amfani da hakan, ya janyota jikinsa. Wata ƙaramar ƙara ta saki, jikinta ya hau tsuma, ta kalli fuskarsa, babu alamar wasa a tattare da shi, wani irin kallo yake yi mata da ba ta san a yaya zata fassara shi ba. Ayshercool 08081012143 Sake ƙasa yayi da muryarsa, ya ce "Ina sake roƙonki, ki bani dama, kin yi mini kuskuren fahimta ne kawai, ban san yaya zan yi miki bayani ba, amma za ki ga komai a aikace" Bakinta ta motsa za ta yi magana, amma a dole ta haɗiye maganar, biyo bayan dogon harshensa da ya saka a kan laɓɓanta. Bayan su Walid sun fita, ya kalli liti ya ce "Ina jinka, me zaka ce mini?" "Wai wannan farar yarinyar yar uwar Nabilan ce ne?" "Eh" "To kuma har muka fito ba ka yi mata magana ba, ka san dai ka fini faraa'a da kalar masu kirki" "In yi mata magana in ce mata me? Ko dai sonta ka ke yi ne?" "To wa ya san mini ma, amma ɗan yi mata magana, gata can sai waya take yi " Walid ya ce "In yi mata magana in ce mata uban me? Kai ka yi mata mana, tun da sonta ka ke yi. Babanta dai tsohon soja ne, wallahi kayi masa shirme sanyawa zai yi kuratan nan, su yi maka dukan jaraba na gaya maka" Liti ya ce "Ta Allah ba taka ba, kuma a yanzu zan nuna maka banbancina da kai" kawai ya nufi in da Walida take waya, tana ta surutu da wata ƙawarta mai kwaliya, tana son tayi booking na bikin Nabila. Ta kammala ta juyo, ta ga Liti a tsaye. "Sannu dai" Ta ce "Yauwwa, ya gida ya shirye-shirye na ganku tare da wanda Arfa zata aura, ina kyautata zaton abokansa ne" Ya girgiza mata kai ya ce "'yan uwansa ne mu" Tayi murmushi ta ce "Masha Allah, Ubangiji Allah ya sa zamu gani" "Amin, ashe tana da ƙanwa babba kamar ke, ai mu ita kawai muka sani" "Ai muna da yawa ma, ba a fiye ganinmu bane, daga makaranta sai gida". Liti ya ce "Masha Allah, ai haka ake so, ki ce tare zamu yi hada-hadar biki, to Allah ya sa a gama lafiya, sunana Abdallah" Ta jinjina kai ta ce "To yaya Abdallah, sunana maryam ana ce mini Walida" Walid kuwa satar kallonsu yake yi, yadda liti ya nutsu yake baza capacity a gaban budurwa, kai ba zaka ce shi ne yake wani iya shegen ba, sai gashi yana ta hira da shi da walida, abin da haryanzu Walid ba ya iya sakin jiki yayi sosai da Shahida. Duk da Nabila ba ta saki jiki gaba ɗaya da Viper ba, amma ta ɗan ji sauƙin damuwar da take ciki, amma har a lokacin faragaba ba ta bar zuciyarta ba. Sai da ta kwana biyu aka sallameta, ta ɗauki hutu a wurin aiki, ta ma daina fita gaba ɗaya, sosai Nabila ta zama so silent, dan ma Sumayya na tare da ita, tana ƙarfafa mata gwiwa. Abbu suna ta shirye-shirye, suna zaune da shi da Viper da daddare, Shahida ma an gama gyara gidan da zata zauna, Abbu ya yi mata sababbin furnitures. A weekend za a kawo kayan lefe. Viper ya dubi Abbu, yadda yake ta kashe kuɗi babu ƙaƙƙautawa, dan haka yake cewa auren yara uku zai yi. Ga Viper, ga Walid ga kuma Shahida. "Abbu muna ta godiya Allah ya saka da alkhairi" Abbu ya ce "Da aka yi me?" "Kuɗin da ka ke ta kashewa a kanmu" "Amfanin neman kenan ai Al'amin, kuma a baya ai ban yi muku ba, Allah dai ya sanya alkhairi" Viper ya amsa da Amin, sannan ya ce "Abbu wata alfarma nake son sake nema a wurinka dan Allah" Abbu har so yake Viper ya nuna yana son yayi masa wani abu, hakan na sanya mishi nustuwa, ya ji cewa lallai ya yafe masa. "Ka ga ramma yar uwata ce, kusan ita da mahaifiyarta sukaɗai suka rage a ɓangaren mahaifiyata, da nake kallo ina jin daɗi. To naga ba tsufa tayi ba, kuma zamanta haka is not safe, na ce dan Allah idan da dama, ban takura maka ba, dan Allah ka aureta. Hakan zai fi sama mata nutsuwa, tun da shi aure garkuwa ne ga mace, duk tsufanta kuwa. Abbu ya shafi gemunsa yayi murmushi ya ce "Yanzu dai ka bari na fara kawar da ku tukuna, ayi wannan maganar" "Eh ai dama ba yanzu ba, na san da hidindimu a gabanka, idan Allah ya sa komai ya daidaita nake nufi" "To ɗan gidan Abbu, Allah ya tabbatar mana da alkhairi" Al'amin ya ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya ƙara arziki" Saura sati ɗaya biki, Viper ya aiko su Walid wurin Nabila, suka yi sa'a Walida ta dawo daga aike. Suka gaisa da su Walid, Liti ya ce "Walida, wurin sisternki muka zo an aiko mu, ko zaki yi magana da ita" "Me zai hana" mintuna goma, sai ga Nabila ta fito, amma yanayin da suka ga Nabila, duk sai jikinsu ya sake yin sanyi, babu wannan karsashin nata, jikinta duk a sanyaye. Haka suka gaisa sama-sama, suka ce Viper ne ya aiko su da kaya su kawo mata. Ruwa da lemo ne carton hamsin, ga buhun fulawa har da kuɗi, wai ta ƙara a abin da za ta yi hidimar biki da shi. Tun da yaje dubata a asibiti, bai sake nemanta ba, ita ma kuma ba ta neme shi ba, ta so kiransa a waya, amma ta fasa ta jira Abba ya dawo ta nuna masa. Faɗa ya hau yi, a kan yadda yake ta ɗawainiya da ɗorawa kansa nauyi, ya kira Abbu yana mita Abbu ya ce "Haba ranka ya daɗe, ni ban ma san an yi ba, kuma abu ne da yakamata ya yi, dan haka ai babu laifi, amma ayi haƙuri idan mun yi laifi" Major ya ce "Ai an riga an zama ɗaya, a din ga sauƙaƙawa juna, wallahi mun tanadi komai na shirin bikin nan, bayan uban kuɗi da ya din ga turo mata na haɗa kayan lefe" Abbu ya ce "Kar ka damu fa, auren fari sadaka aka bashi ai, sisinsa ba ta yi ciwon kai ba, wannan kuwa ya daki jikinsa yayi, sai ya fi riƙewa da kyau" Major ya ce "Aishikenan, Ubangiji Allah ya sanya musu albarka baki ɗaya" Saura sati biyu biki, Abbu ya kai Major da Baba gidan Nabila, flat ne mai kyawun gaske, a cikin unguwar jambulon da ke Kano. Tun duniya na kwance, lokacin da baban su Viper ya fara tashen kuɗi, mahaifiyar su ta sanya ya saya wa Al'amin da Sadik gidaje, ta ce saboda maza ne, idan ya sai musu ya taimake su. A haka kuma da ɗan abin da take samu a hannunsa, da yan sana'oin ta, ta din ga sayen filaye tana ɗan ajiyewa. Aka zo ita ta rasu, Sadik ma ya rasu, dan haka Al'amin bayan gidan da yake da shi, da babu yadda ba ayi da Abbu ya sayar ba yaƙi, Rahila ma tayi ƙulafucin gidan ta gaji. Miliyoyi aka din ga ambatawa gidan ya sayar yaƙi, yanzu gashi ya yi rana, aƙalla Viper yana da gidaje huɗu, da manyan filaye biyu, dan ma ya bi gonar da yake da ita a ƙauye, ya saka an sayar tun Jauhar na raye. A auren nan Viper ba ƙaramin jin jiki yayi ba, duk da Abbu yana taimaka masa, amma kuɗaɗen hannunsa duk sun ƙare, a haka sai da aka sayar da filinsa ɗaya, saboda shi yake taimakawa Walid ma. A duk lokacin da ya tuna a yadda ya auri Jauhar, da a al'adance zai iya cewa auren sadaka, sai ya ji tausayinta, ko da wasa ba ta taɓa nuna masa, ta ji zafin irin auren da aka yi mata da shi ba. Liti duk da yana supporting ɗin Walid shi ma a kan shirin bikinsa, gefe guda yana ta karɓar kuɗi a hannun babansa, ya ƙara ƙawata wurin shayinsu aka mayar da shi joint. Kasancewar Viper ya kwana biyu bai je wurin ba, ranar da Liti ya addabe shi ya je, sai da ya zubar da ƙwalla. JAUHAR MEMORIAL JOINT. Haka aka rubuta a wurin, sannan ga kan famfo ɗaya da aka janyo, liti ya ce "Ga sadaƙatul jariya, mun yi wa ƙanwarmu da ni da Walid, alkhairin Allah ya isketa har cikin kabarinta, ƙoƙarin inganta rayuwarka da tayi, ba kai kaɗai ta yi wa ba, har da mu". Cikin wurin duk an rubuta, dan Allah ku karanta wa marigayiyya Jauhar ƙulhuwallahu ƙafa uku, Allah ya jiƙanta da sauran musulmi baki ɗaya. Idan Viper ya ce yana da kalamai, ko wani abu da zai yi, domin nu na godiyarsa ga bayin Allan nan da suka kasance da shi, a halin tsanani da na jin daɗi, to ya yi ƙarya. Su Abba sun yaba gidan Nabila ba kaɗan ba, manyan ɗakunta uku, da falo biyu, ga komai a wadace dai-dai misali. Duk da ba a rasa 'yan tsegumi ba, da aka je jere, da suka din ga gulmar, a iyayi irin na Nabila, da yadda ta din ga dating manyan mutane masu kuɗi, ba su yi zaton zata ƙare a wannan gidan ba, duk da shi kansa yadda ake cewa ɗan daba ne, sun zata mara galihu ne da abin yi, dan sun raina kansu da suka ga gidan da ɗan daba zai saka amarya a ciki. Nabila dai ta kama wuridin ya haiyyu ya ƙaiyyum bi rahmatika astagis, aslih lii sha'ani kullahu, wala takilni ila nafsi, ɗarfatu ainin. Domin samun mafita a kan maganar aurenta da Viper. ***** Rana ba ta ƙarya, sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, aka fara gudanar da biki, shi kansa Viper yayi rama saboda rashin hutu. Dinner da kamu, duk amare ne suka je ba angwaye, Nabila ta yi kyau sosai, farar fatarta tayi kyau da kaya da kuma kwalliyar da aka yi mata, haka ma Shahida ta sha kyau. Sumayya ma sai kai wa da komowa take yi, tayi kyau sosai da sosai. A hada-hadar kai komon biki, liti suka ƙara sabawa da walida, har da karɓar lambarta. Walid ya ce "Zaka gane kurenka, ka gama yi wa Nabila rashin mutunci, ka zo kana bin ƙanwarta, Allah ya kawo mata lokacin ramawa" "Kai dai ɗan baƙin ciki ne, saboda Allah ya kawo maka lokacin aure, duk sai ku tafi ku bar ni, to baka isa ba". An ci an sha, an yi biki lafiya aka kammala lafiya, da yamma aka fara shirin kai amare. Nabila na ta kuka, ba kuma wai dan zata bar gidan nan ba, kawai ji take auren Vipern tsoro yake bata ba na wasa ba. Abbu ya yi wa Viper da walid nasiha sosai da sosai, haka Shahida ya gargaɗeta a kan kar ta biye wa mahaifiyarta, ta ɗorata a kan keken ɓera, ta kashe mata aure. Ranar da aka ɗaura auren su Walid, a ranar Viper ya yi walimarsa, tare da abokansa, wanda dama su Walid ne, sai kuma sojoji. Amma ba a manta baya a harkar, dan hatta tsofaffin yaransa 'yan cau-cau, da marasa ji sai da suka halatta, sai dai a wannan karon, ba rashin hankali aka yi ba, kamar yadda na auren jauhar ya gudana ba, kowa taitayinsa ya shiga, mussaman da sojoji suka cika wurin. Nabila ta rirriƙe sumayya tana kuka, ita ta zauna da Nabila, har bayan isha'i, kowa ya watse, ta kira wands zata aura, Faruk wanda ɗan uwa ne ga Alhaji mu'azzam. Amma fafur Nabila ta hanata tafiya, sai da Viper ya shigo. Kamar yadda ya saba komai nasa daban, shikaɗai ya shiga gidan, sai da Sumayya ta tafi ya rufe gidan, ya tsaya yana ƙarewa gidan kallo, ko ina hasken fitilar solar. Ya tuna lokacin da ya je wa jauhar, butsu butsu, Walid ne ma ya takura masa, ya haɗo shi da kayan dauɗarsa ya rako shi. Ɗan guntun murmushi ya yi, ya shiga ya iske Nabila a bedroom, ta ƙunshe kanta da mayafi. Ya ce "Ki taso ki yi alwala mu yi salla" a hankali ta motsa, ta saukko daga kan gadon, idanunta duk a kumbure, rabon da ya ganta tun a asibiti, ko ta waya ba su sake magana ba. Ta je ta fara yin alwala, shi ma yayi ya fito, amma ya ga ta ja ta tsaya a gefe. Sai da ya raɓata ya tayar da sallar sannan ta bi bayansa, bayan sun idar yayi addu'a gwargwadon abin da ya iya. Ya janyo mata ledojin da ya shigo da su, ya ce "Bismillah ga abinci, me zaki ci a nan?" Ta girgiza kai ta ce "Ba komai" "Saboda me?" "Na ci abinci a gida" Kawai ya ce "Ok" Da ya motsa sai ta zabura, gaba ɗaya ta takura kanta, ta hana kanta sukuni. Ya tashi ya bar mata ɗakin, sai bayan awa guda, sannan ya koma, ta kwanta a ƙasa ta lulluɓe jikinta da lafayarta, sai dai tana jin motsinsa ta sake zabura ta tashi zaune. "Ki je ki kwanta, tun da bacci ki ke ji" sai da ta ɗan yi jimm, sannan ta tashi taje ta kwanta. Ya ɗaukko sabon bargonta ya ƙara mata, tana kallonshi yana rage kayan jikinsa, zuciyarta na tsananta bugawa tana rarraba ido, yana juyowa suka haɗa ido, tayi wuf ta shige cikin bargo. Yana kashe fitila, ta tashi zaune, yana kallonta, ya zo ya samu wuri a farkon gadon ya kwanta, amma taƙi kwanciya. A ransa ya jinjina hali irin na Nabila, ya san dai ba ta isa hana shi abin da yayi niyya ba, amma tabbas zai sha fama da taurin kai. A yanayi irin na Nabila, da ta rayu cikin ƙabilu, har ta bar Nigeria ta je tayi karatu, da yadda take gudanar da rayuwarta, sai ka zata a waye take, koma mutum yayi mata kallon mutuniyar banza, amma zunzurutun tsoro da tashin hankalin da yake tattare da ita, ko taɓata yayi sai ta kusa tara masa jama'a, abin da ba ta sani ba shi ne, zai iya shanye koma me yake ji ya rabu da ita. Kamar dai a zamansa da jauhar, da sai da ya fara gani a idonta, duk da shi akwai sabo sosai da sosai a tsakanin sa da ita. Ta sauran hasken da yake shigo ɗakin yake kallon yadda take gyangyaɗi a zaune, har ta gaji ta tuntsura, amma da ya juya sai ta tashi. Gidan ango Walid kuwa, halin ya ci gaba da gwadawa, shi ba tsoro ba, shi ba matsananciyar kunya ba. Bayan sun yi salla sun idar, ya gabatar mata da kaza da ɗan abin da ya sauwwaƙa. Ba ta ci sosai ba, su ka ɓuge da hirar yadda biki ya gudana. Ganin ta ɗauki kayanta ta shiga toilet, ya sanya ya bata wuri, yana sake ƙare wa gidan kallo, cike da nishaɗi. Da ya koma ta canza kaya, zuwa doguwar riga, ta bacci, da hijjabi. Sai wani raɓe-raɓe yake, kamar mai shirin aikata zunubi. Bacci ne yake shirn ɗibarta, saboda a gajiye take. Kwanciya Walid ya yi a bayanta, da kayansa na angwancin da komai, duk da yadda rigar ta dame shi, sai da ya ji uwar bari ya cireta. Ƙamshin turaren da take yi ne, yake ta ci gaba da fizagarsa, sai godewa Allah yake yi, wai yau shi ne yayi aure. A hankali ya kai hannunsa kan na Shahida, kamar mai taɓa wuta, ta buɗe idanunta, taga ɗakin ya gauraye da duhu. Ta ɗan motsa kaɗan tana ƙara jinjina tsagwaron kunya irin ta Walid. "Shahida" "Na'am" "Dan Allah ki na so na, ko kin aureni saboda kawai Viper ne ya baki umarnin hakan?" Sautin murmushinta ya ji, ta ce "Ba na ce ka daina faɗar sunana ba, idan ka faɗa sai na ji kamar ba ka so na, saboda yaya Aminu kawai ka aure ni" Da sauri ya ce "A'a ina sonki sosai, waye zai ce ba ya son mace kamar ki?" "Kai manaz tun da kana faɗar sunana" Ya ce "Na daina, sweetheart ki ka ce na ce ko?" Sosai take yi masa dariya, ta ce "Au ni na ce ma, ba kai ka yi niyyar kirana haka ba" Walid ya ce "Daga cikin zuciyata ya fito, ki yi haƙuri wallahi duk ban iya irin wannan bane ba" Shahida ta ce "Yaya ya gaya mini ai, ku mazaje ne, ba ku iya soyayya ba, amma ni gaskiya ka koya" tayi maganar a shagwaɓe. "In sha Allah, zan sayo littafi ki din ga karanta mini kullum ina haddacewa" tayi murmushi tana jin yadda yake ta wasa da yatsun hannunta. "Shahida ban taɓa tunanin rayuwa zata canza, har na yi iyali ba, babu abin da zan ce wa Allah sai godiya, kuma babu abin da zan cewa Viper, sai Allah ya sa ya gama da duniya lafiya, bani da bakin da zan yi masa godiya, ya mayar da ni cikakken mutum" "Ramawa kura aniyarta aka yi, ku kuka fara riƙarsa a yadda yake, ku ka mayar da shi mutum, Allah ya ƙara haɗa kanku" "Amin sweetheart" dariya ta yi masa jin ya ce sweetheart. Walid ya gama noƙe-noƙen da jin kunyar, ya raya darensa. Sai dai ya shiga lissafi, duk da shi dai bai san dawan garin ba, amma kamar akwai banbanci tsakanin budurwa da kuma bazawara, amma bai mayar da hankali a kan tunanin hakan ba, saboda kukan da Shahida take yi, ya din ga bata haƙuri kamar wadda ya tafkawa laifi, har sai da ya bata tausayi. Washegari da safe ma, ita tana jin nauyinsa, shi ma sai sinne kai yake yi, lokaci lokaci yana sakin murmushi. Liti kuwa da kyar yayi bacci, saboda babu Walid babu Viper, yayi ta mita, wai suna can tare da bargo mai numfashi da sabuwar katifa, shi yana nan ya kasa bacci. Da sassafe Liti ya kira Walid a waya, Walid bai watstsake daga bacci ba ya ɗaga ya ce "Lafiya?" "Au haka ma zaka ce? Koma kira ni ka ji yaya nake?" Walid ya ce "Haifarka na yi da zan kiraka da sassafe na ji yaya ka ke?" "Allah sarki ni, wato kai yanzu ka yi 'yanci, yayi kyau, na ce ba, ka rage mini kazar ko kuma yaya?" "Eh, ta na wurin mai zamani ka kira shi ka karɓa" Liti ya ce "Ai da shi muka fara yin waya, Abuja fa zai tafi yau" Da sauri Walid ya tashi zaune ya ce "Haba dai?" "Wallahi haka ya ce mini, cikin dare aka tura masa saƙo, gashi har aka gama bikinsa ɗan mama baya nan" "Amma shi aikin nasu babu hutu kenan? Mutum yayi aure amma ace ya fito washegari" "Kai ma dai ka faɗa" "Bari na kira shi" sun yi sallama da liti, amma ya kasa kiran Viper, saboda kunya, shi tunani ma yake idan ya koma kasuwa ko zai iya kallon Abbu. Gidan Ango Al'amin kuwa, bayan sallar asuba Nabila ta koma bacci, ganin Viper bai dawo ba. Ƙarfe tara ta tashi, still baya ɗakin, ta kulle bedroom ɗin, ta shiga banɗaki ta yi wanka, ta duba jakarta ta ɗauki brush ta wanke bakinta. Ta canza kaya ta fita falo, tana kallon gidan. Kitchen ta leƙa, ta tarar har ya dafa tea, tana tsaye ta ji ya buɗe ƙofar falo, falon ta dawo a dai-dai lokacin da ya shigo. Ta ɗan maze ta ce masa "Ina kwana?" "Ban ganshi ba" ya amsa mata, tare da wucewa digning, ya ajiye ledar hannunsa, ya dawo in da ya barta ya ce "Ga abin breakfast can, kazarki kuma da baki ci ba, tana kitchen. Ni an turo mini saƙo tun cikin dare, ƙarfe sha biyu zan bi jirgi na koma Abuja. Ba ta san lokacin da ta ce "Saboda me?" ba. "Harkar aiki" "A kawo ni juya yau kuma ka tafi, yaushe zaka dawo?" "Ina ruwanki da lokacin da zan dawo? Dama ai ba ƙaunar ganina ki ke yi ba, tun da an aura miki annoba, idan na matsa sai ki sarara" Cikin kuka Nabila ta ce "Ai dama na sani, a haka ka ke cewa na baka chance ɗin, ko na baka chance ɗin, na san babu wani da zai canza, ba na gabanka, ba ni da wani muhimmanci a tare da kai, am regretting this marriage" Shareta ya yi ya wuce cikin ɗaki, ita da ta nuna ba ya gabanta, ko menene na ɗaga hankalinta kuma, dan kira shi wurin aiki oho mata. Duk da a zahiri shi ma bai so hakan ba, amma dolensa ya tafi muddin yana son yin galaba a kan Indabo, ta wani fannin kuma, yadda Nabilan ke treating ɗin sa, gara ya tafi kawai ya rabu da ita. Da fari kuka ta zauna tana yi, daga baya ta ga kamar ta faɗo ne, sai ma ya rainata, shi bai damu da ita ba, ita kuma ta damu da tafiyar sa. Ta haɗa abin kari tana karyawa, kamar ta na cin magani, ya sake fitowa ya fita, aka jima sai gashi da kayan abinci niƙi-niƙi. Ƙarfe sha ɗaya ya sameta a ɗaki, ta ɓuya tana matsar hawaye. Kamar bai gani ba, ya ajiye mata kuɗi ya ce "Na san maybe zaki yi baƙi, ga kuɗi nan, idan kina buƙatar wani abu, na san kirana a waya abu ne mai wahala, zaki iya kiran wanda ki ka ga ya dace kin yarda da shi, ya kirani ya sanar mini" har ya bar ɗakin ba ta ce masa uffan ba. Ya saɓa jakarsa ya fita, zuciyarsa na yi masa zafi, yanzu yana ƙoƙarin gazgata Nabila ba ta ƙaunarsa. Tafiyarsa babu jimawa kuwa baƙi suka din ga zuwa, dan haka sai damuwar ta ta ta ragu, sai dai ana watsewa komai ya dawo mata. Walid kuwa hankali kwance ya ci gaba da shan sharafinsa da amarya Shahida. Ranar da zai koma kasuwa, ta sha dariya har da riƙe ciki, wai kunya yake ji ya fita kasuwa ya haɗu da Abbu ma. Da kyar ya samu ya fita, Allah ya sa ranar Abbu bai je kasuwa ba, sai dai duk bayan mintuna kaɗan, yana maƙale da waya yana kiran Shahida, sai da ya ji kamar ya janyo yanna ta yi ya koma gida. Sai da liti ya gaji ya fara zage-zage da faɗar maganganu, Walid kuwa yayi masa banza, sai daga ƙarshe ya ce "Zafin gwaurantaka ke damunka, ba zan kula ka ba" Sannu a hankali baƙi suka fara ɗauke ƙafarsu daga zuwa gidan Nabila, hakan ya fara damunta, ga Viper tun da ya tafi babu ko flashing, hakan ya ƙara ƙona mata rai, ita kuma ta kira shi, gani take ta faɗo. Sumayya dai ta ci gaba da rarrashin Nabila, kusan duk kwana biyu sai ta zo wa Nabila, dan ta gaya mata Viper ya gari. Ita ma a hankali ta rage zuwa, an doshi sati uku, babu Viper babu labarin sa, ko baccin kirki ba ta yi sai aikin kuka, idan ta gaji kuma sai ta yi ta tasbihi, saboda yana daga abin da yake sauke mata fushi da wuri. Babu tsammani ta ji ana buga mata gate, ta tashi ta fita tana tambayar waye?. "Buɗe ki gani" tana buɗewa ta ga Walid da Shahida, murmushi tayi tana yi musu maraba. Sun yi ƙalau da su, daga shi har ita, Walid ya kuma nutsuwa, kuma cikin manyan kaya yake, yanayin yadda suke magana akwai fahimtar juna a tsakaninsu. Ita kuwa an zubar da ita a cikin gida, ya tafi aikinsa ko ta kanta baya waiwaya. Walid ya ce "Bari na tafi kasuwa, da yamma na dawo mu tafi, dama Viper ne ya ce wai lallai in kawo miki ita, ta tayaki hira, kaɗaici ya dame ki, na ce masa to ya dawo mana" Nan dai ya bar mata Shahida, shi kuma ya tafi. Shahida ta ce "Anty Nabila, maman dr. Duniya ce, ai ni mun ƙulla alaƙa da ita, ai yanzu na san nayi aure, wannan auren mai kuɗin duk ba shi ne ba" Nabila ta yi murmushi ta ce "Au da ba aure ki ka yi ba?" "Taɓ, aka gama yi mini banke-banken magani, da shi da babu duk ɗaya, magani ya kusa illata ni, sai da na kwanta a asibiti, kuma na kasa faɗar abin da ya faru. Ga yan uwansa masifaffu, wai yana ta aure mata ba haihuwa, shi bai gaya musu shi ne mara amfani ba. Na sha wahalar auren nan, shekara uku sai da na ci na yi kallo, na zauna babu banbanci da ina gida, kuma kowa gani yake nayi aure a gidan hutu. Na cire kunya na gaya wa mama, wai sai cewa tayi, Allah ya rufa mini asiri zan tona wa kaina, nayi nayi ya sake ni yaƙi, ni kuwa na kaishi kotu, na ga zai saye su da kuɗi, na samu Abbu na gaya masa, aikuwa yayi ta faɗa" Nabila ta waro ido ta ce "Abbun ki ka gaya wa wannan maganar?" "Eh mana Anty Nabila, da ace masa gani can da aurena ina ɓarna fa? Idan cin abinci da kallo na je yi, in zauna a gidanmu mana" Nabila ta ce "Gaskiya tun da na ji Hafsa ta yaba, kema kin yaba, na ƙara yadda da kayan maman dr" "Sosai fa, zata baka abin da ya dace da kai, da aka yi mini auren fari, ai wata jahila aka samu ta din ga jibga mini kayan shashanci suka kusa kashe ni, ai maman dr tayi a rayuwa. Ni gidan Yaya muhsin duk da bashi da ƙarfi, ya fiye mini gidan tsohon mijina sau dubu, ga ci ga sha ga kwanciyar hankali, gashi lafiyayye, ban yi gyara a banza ba" Waro ido Nabila ta yi ta ce "Kin fi ƙarfina Shahida" "Hmm ba zaki gane ba, matan da suka tsinci kansu a irin halin da na taɓa tsintar kaina, sun san takaicin abin nan. Kana gidanku baka san komai ba dama, ya fi sauƙi hankalinka a kwance yake, amma an aurar da kai, mutum ya san ba shi da lafiya, saboda zunzurutun zalunci, ya aureka, kuma yan uwansa su addabeka, baka haihuwa, wallahi na kusa gaya wa babarsa ranar da aka ishe ni, kawai nayi shiru" ('yan uwa kar ku bari a baku labari, ko kuma a bar ku a baya, ku garzaya ku jarraba, kayanta, ga kyau ga kuma inganci 0706 971 1327) Nabila ta ce "To Allah ya kyauta, Allah ya ƙara muku zaman lafiya da fahimtar juna, tun da kin samu abin da ki ke so" Dariya tayi, ta ce "Amin, ina nan ina ta kwantar da kai ina lallaɓa abina, ko ƙuda bana son ya taɓa mini shi, ina matuƙar son sa da tausayinsa" Nabila ta ce "Yakamata, ai Walid mutum ne na gari" Sun sha hira sosai da sosai, dan sam Nabila ba ta bari, Shahida ta fuskanci damuwa a tattare da ita ba. Bayan tafiyar su, da daddare ta rasa abin yi, ta buɗe wardrobe ɗin Viper, ta sauke kayan tana gyarawa. Wani ƙaramin littafi ta gani, ta ɗauka ta fara dubawa. "Wannan littafin na master ne, kar ka manta ka karanta shi safe da yamma" Azkar ne aka rubuta shi, na safe da yamma da hausa, sai kuma Addo'in kwanciya bacci. "Ka kula mini da kanka sosai master, duk lokacin da ka karanta, ka yi mini addu'a" Ƙasa sai ta zana heart da sunansa, irin da na soyayyar ƙuruciyar nan. Shafa littafin Nabila ta din ga yi tana kuka, ta ce "Allah ya sa auren mijinki, kar ya zame mini cin amanarki 'yar uwata, Allah ya sa ba ƙaddarar auren nan ne ya sanya ki ka bar duniyar nan ba, ina ƙaunarki duk da ban sanki ba" Sosai Nabila ta yi kuka, mai ban tausayi, daga bisani ta tashi jiki a sanyaye. Kamar wadda aka yi wa nasiha, washegari, ta tashi da matsananciyar kewar Viper, babu tunanin komai, ta ɗauki waya, ta din ga kiransa, amma wayarsa a kashe. Kawai sai hankalinta yayi matuƙar tashi. Madam halima ce ta kira Nabila, suka gaisa ta ce "Nabila, gobe Joseph zai zo da safe, zaku tafi Abuja, Viper babu lafiya" Ƙirjin Nabila ya buga da ƙarfin gaske, ta ce "Meya same shi?" "Ban sani ba, Joseph ne ya zo yake gaya mini, dan haka ki zama cikin shiri" kuka ta saka wa madam, tana tambayar ta, idan wani abun ne ya same shi ta gaya mata, amma ta ce mata ba ta sani ba. Ana idar da sallar asuba ta shirya, cikin matsanancin tashin hankali, addu'a kawai take yi Allah ya sa yana lafiya. Ta waya suka din ga communicating da Joseph, ya zo gidan, ya ɗauki Nabila suka tafi, sai da ta tambaye shi ko ya san wani abu a kai, amma ya ce mata bai sani ba. Sumayya ce ta kira Nabila, ta ce mata maza ta hau social media ta duba meke faruwa. Hannunta na rawa ta buɗe tana duddubawa, wai tsohon riƙaƙƙen ɗan daba Aminu Viper, ya koma ɗan ta'adda, bayan da yayi attacking ɗin manyan mutane ciki har da honorable Indabo, da bindiga a wani guset house da yake Abuja. "Impossible, this is not true, Vi ba zai yi haka ba, dole akwai wani abu a ƙasa" Sai daf da azahar suka isa barrack ɗin da yake aiki a Abuja. Nabila sama-sama take numfashi, a ganinta gawarsa kawai za su nuna mata. Wani ɗaki aka shigar da ita, yana kwance a kan gado, ana ƙara masa jini, da gudu ta ƙarasa gaban gadon da yake, bakinta na rawa tana faɗin Innalillahi wa Innalillahi raji'un. An nannaɗe kafaɗarsa da bandeji, ga cikinsa gefe a kumbure. Alamu ya nuna harbinsa aka yi a kafaɗarsa. "Vi, ka tashi dan Allah ka tashi" "Madam ki yi haƙuri, bai daɗe da samun bacci ba" Ko ta kan mai maganar ba ta bi ba, ta ci gaba da kuka. A hankali ya buɗe idonsa, ya ɗago ya kalleta. "Vi, meyafaru haka, garin yaya aka harbeka, da gaske zuwa ka yi ka kashe indabo, meyasa zaka yi attacking ɗin sa haka?" Lafiyayyen hannun ya ɗago, ya shafi fuskarta, ya ce "Aiki mu ka je, ban yi attacking ɗin kowa ba. Mun yi negociating da wasu hukumomin na tsaro ne, aka je gidan, amma an ce na yi laifi, zan iya fuskantar hukunci, na yi harbi ba a bani umarnin hakan ba, duk da yaransa sun yi yinƙurin kashe ni. An kama Naja'atu Bunkure a gidan, da ƙanan yara mata da ake lalatawa da kuma maza, gidan da aka yi sanadiyar ran Nura ne, kuma mun kama makamai a gidan, da wasu manyan ƙusoshin gwamnati duk a gidan. Hukumar soja ba sa zargina sa ta'addanci, wannan sharrin media ne, da nake kyautata zaton mutanen Indabo ne suka saka ayi mini hakan, hukuncin da zan fuskanta na harbi ne ba ayi mini uzuri ba, ina da abubuwa da yawa da tun a baya na so mu tattauna, amma baki bani chance ba, baki bani da ma ba Abla, akwai abubuwan da nake buƙatar aiki da ƙwaƙwalwarki, saboda ta kan yi mini jagora a wasu abubuwan, amma ki ka ƙi saukko ki fahimce ni" Ƙanƙame shi ta yi tana kuka ta ce "Am sorry Vi, ka yi haƙuri dan Allah, amma zan ɗauki kowane irin mataki, wallahi babu mai hukunta mini kai, wahalar da ka sha ma ta isa haka, wace irin ƙasa ce wannan? In dai ina raye babu wanda zai yi maka wani hukunci babu shu" Ya saka hannu yana shafa kanta ya ce "Dan Allah ki zauna tare da ni abla, zamanki a kusa da ni, yana bani ƙwarin gwiwa ina jin am safe idan muna tare, tun ba yanzu ba Please" ya ƙarasa maganar muryarsa na rawa. *GA MASU JIRAN DOCUMENT, ZA SU IYA PAYMENT YANZU, FEW PAGES YA RAGE, ONGOING PAGES NE 500 COMPLETE DOCUMENT KUMA 1K. VIA 0009450228 AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143 Ayshercool 08081012143 "I promise that, ina tare da kai ɗari bisa ɗari, komai tsanani da wahala, is enough yakamata ka huta haka, masifun nan sun yi yawa" Ya sauke ajiyar zuciya ya ce "Ina ga haryanzu sakamakon laifuffukana ne suke ci gaba da bibiyata". Ta ce "A'a, Allah ba azzalumin sarki bane ba, kuma yana son bayinsa masu neman gafararsa. Wannan wata jarrabawa ce ta daban, kuma zamu cinyeta ita ma in sha Allah, sannu Vi" ya jinjina mata kai kawai bai sake cewa komai ba. Wayarta ta ciro, ta lalubo lambar Alhaji mu'azzam, ya ɗaga tare da yin sallama, ta amsa masa ta ɗora da cewa "yallaɓai ka ga abin da ya faru da Viper?" "Wallahi ɗazu na gani Nabila, raina yayi mummunan ɓaci, na je Kano ne, amma anjima kaɗan zan shigo Abuja in sha Allah, kuma already na yi magana da ministan tsaro ma, za ayi bincike a kan lamarin" "Wane bincike kuma, ana cewa wai sai an hukunta shi yayi harbi ba bisa ƙa'ida ba, ga harbi da aka yi masa, ni idan har haka aikin yake, kawai zai ajiye musu aikinsu, wannan wahalar ta isa haka" "Ki yi haƙuri Nabila, na san halin da ku ke ciki, na kuma san wahalhalun da ya sha, duk kitumurmurar indabo ce, ina kyautata zaton an ce an sake shi ma, sai dai na zo kawai" tana cikin maganar wasu sojoji su uku suka shigo, da alama manya ne sosai a cikin rundunar tsaro, ta katse wayar. Joseph ne ya ƙame ya sara musu, sannan ya kalli Nabila ya ce "Ko zamu ba su wuri?" Ko kallonsa ba ta yi ba ta ce "Ba in da zani". Ɗaya ya ce "Sannu Viper" Viper ya jinjina kai sannan ya ce "Thank you Sir" Nabila ta ce "Da gaske ne wai sai an hukunta shi saboda yayi harbi?" Suka kalleta gaba ɗaya, ɗayan ya ce "Muna tattaunawa a kan lamarin ne, an ce ba shi yayi harbin ba, Dss ne, kuma mun duba bindigarsa, yayi harbi da bullet biyar" Ta ce "Yanzu idan na ɗauki bindiga zan harbeka, ga bindiga a hannunka tsayawa zaka yi sai wani ya baka order zaka kare kanka?" Ba ta damu da mamakin da ya bayyana a kan fuskokinsu ba ta ci gaba "A matsayina na lauya nake yi muku magana, wadda ta san 'yancinta, ni ba soja ba ce ba, kar ku yi expecting wata special girmamawa daga gare ni, na san ƙarshenta dai ace a kashe ni. Yanzu da an kashe mini shi, gawarsa kawai zaku kawo mini kuna yi wa gawar faretin banza da na wofi, babu lallai a samu hukumar ta sake bi ta kaina a matsayina na matarsa. Masu laifin da ya taimaka aka kama, ba ƙasa ya yi wa aiki ba? Harbin da aka yi masa bai isa ba, kuma sai an yi masa wani hukunci, ga suna an ɓata masa an kira shi da ɗan ta'adda amma ba ku ce komai ba" Viper ya ce "Nabila" "Ka ƙyaleni Vi, sai dai a kashe ni, kun san abin da ya yi going through in his life, washegarin tarewata da aurenmu, ku ka ce lallai ya zo bakin aiki, yazo kuma yayi abin da ku ke so, kuma this is what he deserves, da haka za a saka koya wa matasanmu ƙauna da kishin ƙasa? Masu laifi na sharholiya masu kare ƙasa ana gana musu azaba, a kan laifi ƙanƙani, i will fight for his right" numfashinta sama yake yi sosai cike da ƙunar zuciya da takaici. Viper kuma ba shi da ƙarfin da zai hanata, saboda jirin da yake ji, da kuma jinin da ake ƙara masa. Ɗaya daga cikin sojojin, da Nabila ke kyautata zaton shi ne babbansu, sai ya yi murmushi, cikin harshen hausa ya ce wa Viper "Kai ka auro zakanya kamar kai, she's lioness and fearless, i like her confidence. Madam, we are working on your husband issue, muna supporting ɗin sa, a kan ayyukan da yake yi, kin san mu bamu da hurumin kama mai laifi, sai dai muna hana yi wa ƙasa ɓarna. Mun yi haɗin gwiwa da wasu hukumomin, Viper shi ya gano gidan, kuma tare da shi aka je, a ƙoƙarin kama masu laifin, aka fara harbe-harbe. Kuma mu bamu fitar da report na ga abin da ya faru ba, and abin da viper ya yi bamu gama yanke hukunci a kai ba, kin ɗauki zafi da yawa ki yi haƙuri, Viper aikin sa ba zai iya ajiye shi yadda ya ga dama ba, ya san dokar aikin ai. Kuma zamu bincika duk wanda yake da saka hannu, wurin wallafa wannan labarin zamu baki dama, ki kai ƙararsa ki yi haƙuri" Joseph kansa da ya fara tsuma, bai san hukuncin da za a iya yi wa Nabila ba, wannan kwarmaton da tayi ba, amma abin mamaki, sai ya ga an ɓuge da rarrashinta. Hawayenta take gogewa, amma sun kasa tsayawa, saboda wani irin matsanancin tausayin Viper, da ya takura zuciyarta, ya wahala da yawa. Ɗaya sojan ma, rarrashinta ya din ga yi, yana kiranta da 'yar sa. "Da kin san matsayin da mutane masu muƙamin Viper suke da shi a rundunarmu, da baki ce ya ajiye aiki ba, amma muna baki tabbacin, zamu san abin yi a kan sa" Suka gama maganganun da za su yi, da rarrashinta suka fita. Matsawa ta yi sosai jikinsa, sai bin sa take da ido. "Abla" "Na'am vi" ya juyo a hankali ya riƙeta ya ce "Ki zauna a kusa da ni, kar ki je ko ina dan Allah" "Ina tare da kai in sha Allah vi" "'yar madara ta tafi ta bar rayuwata da duhu, kin fara hasakata amma kina ta so kema sai kin bar ni, Please" Ta katse shi ta hanyar cewa "Vi dan Allah ka yi shiru, Allah ya baka lafiya na ɗaukeka mu tafi, Allah ya baka lafiya" Ya sake cewa "Amin, indabo azzalumi ne abla, an kama shi, amma na san sakinsa za su yi, na yi iya yi na, na bar wa Allah sauran" Nabila ta ce "In sha Allah kuma zai isar maka" Ta lallaɓa ta tashi, ta yi alwala ta yi salla, ta zo ta yi masa alwala,  ya gabatar da salla yana kwance. Wasu sojojin ne suka sake shigowa su biyu, ba su ce mata uffan ba, aka cire masa jinin da yake shiga jikinsa, kasancewar ya ƙare, suka ɗaga shi zaune, ya jingina da jikin gadon. Suka sara masa, sannan suka juya za su tafi. Viper ne yayi gyaran murya, suka tsaya suka waiwayo. Yayi wa ɗaya alama ya zo, ya tako ya ƙaraso, Viper ya nuna masa abincin da suka shigo da shi. Babu musu sojan ya buɗe kowanne ya ci, ya rufe. Da hannu ya yi musu umarni suka tafi. Nabila tana jejjera masa sannu, ya kalleta ya ce "Ga abinci nan ki ci" Ta ce "A'a sai dai kai na zuba maka ka ci" Ya girgiza kai ya ce "Na ƙoshi" Cikin damuwa ta ce "Ka ƙoshi kuma, vi kamar dai akwai wani abu kuma da yake damunka" ya ɗago ya kalleta. "Menene ka gaya mini mana" "Ba komai" ya faɗa a taƙaice. Ta marairaice ta ce "Please, Vi menene ka gaya mini" "Jikina ne kawai babu daɗi" "Sannu, bari na zuba maka, ko kaɗan ka ci" Baya son ta ci gaba da takura shi da tambayoyi, dan haka ya daure ya din ga haɗiyar abincin, tamkar yana haɗiyar magani. Ya gama ta bashi ruwa, ta dubi hannunsa ta ce "An cire bullet ɗin ne?" Ya jinjina kai ya ce "Tun ranar aka cire". "Amma yaya aka yi ka je gidan da kanka, har tsautsayin nan ya faru?" Ya ɗan numfasa ya ce "Tun bayan rasuwar Nura, da ya gaya mini in dw zan samu Simon, na je na same shi. Shi ne ya gaya mini in da gidan yake, da abubuwan da suke wakana a gidan. So ban yi wani abu a kai ba, har tsautsayin nan ya faru, so bayan nan na daɗe ina fakon gidan, ina da informers ɗina a kan gidan. Sai dai yadda ake gudanar da laifuka a gidan, akwai tsari da taka tsantsan ɗin da babu lallai a gane, tun da da haɗin kan wasu daga cikin jami'an tsaro ake abin da ake yi. Nayi magana da shugabannina, muka yi haɗin gwiwa police da DSS, sai da na tabattar da Indabo yana gidan, muka je operation, sai dai bayan mun shiga, wasu daga ma'aikatan gidan suka far mana da harbi. An kama Indabo Naja'atu ma tana gidan, da wasu manya a ƙasar nan, police sun tafi da su, amma bana tunanin za ayi wani dogon bincike, rahotannin da na samu, kamar an ce an sake shi ma, amma bani da tabbas. Ina takaicin mutum kamar Indabo ace ya ci bulus a kan abubuwan da ya aikata, amma babu komai" "Wallahi ba zai ci bulus ba, dole ya girbi abin da ya shuka ko da me yake yawo" "No, kar ki kuskura ki ce zaki yi wani abu, yanzu ma abin da ki ka yi, ikon Allah ne ya tsallakar da ke, kin san suwa ki ka tsaya a gabansu ki na faɗar maganganu kuwa? Bani da ƙarfin hana ki a lokacin, amma da sun yi yinƙurin yi miki wani abu, to da zan nemo ƙarfin duk in da yake na baki kariya, ko da kuwa hakan na nufin na rasa raina ne. Gidan soja ne nan, ba a misbehaving, idan ki ka yi dole na karɓi hukuncin da za ayi miki. I don't know why you are so much lucky" "I am lawyer, 'yanci na sani, dan haka ba ruwana da dokar koma gidan waye, mijina nake son ya samu 'yanci" Murmushin gefen baki yayi ya ce "Kamar gaske" "Da gaske nake Vi" "Na ji amma ban yarda ba" Alhaji mu'azzam ne yayi sallama ya shigo, suka amsa gaba ɗaya, ya ƙarasa suka gaisa da Viper. Cikin damuwa ya ce "Sannu Viper, ya jikin?" "Alhamdilillah" "Ashe abin da ya faru kenan, nayi magana da shugabannin naku ai, kuma ministan tsaro ya bayar da umarnin lallai su yi magana su wanke ka" Nabila ta ce "Alhamdilillah, har shi ma ya ji?" "Eh tun kafin na zo muka yi waya ai, kuma zamu gurfanar da gidan jaridar da suka sanar da wannan labarin ƙaryar, dan na san biyansu aka yi suka yi hakan". Viper ya ce "Wai da gaske an saki Indabo?" Kankarofi ya jinjina kai ya ce "Ai ba a bari ma an sanar da ainihin abinda ya faru ba gaba ɗaya. Amma tabbas an bayar da belinsu, Bunkure ce ba a saki ba, dama ita tuntuni kotu ta bayar da umarnin a nemo ta, duk in da take a gurfanar da ita a gabanta. Ka yi haƙuri na san abin da ka ke ji a ranka, amma ina mai tabattar maka da wahalarka ba zata tafi a banza ba, kana yi wa ƙasa hidima da ranka da jikinka, dan haka dole ayi maka wani abu na girmamawa" "Bana buƙatar komai, dama babban burina in ga an hukunta indabo, tun da ba zan samu hakan ba, shikenan na haƙura" "Kar ka yanke tsammani Viper, tabbas indabo yana da connection da manyan ƙasar nan, da suke aikata ɓarnar su tare, shiyasa baya taɓuwa, duk da Nabila tayi breaking record ta jijjiga shi, alhalin yana kan kujerar mulki, kin yi namijin ƙoƙari sosai, amma ka bar shi da Allah, kai fa ko iya haka ka tsaya ka ɗauki fansa, ka jira kaga yadda Allah zai yi da shi kuma". Viper ya sunkuyar da kai yayi shiru, sai huci da yake yi. Nabila ta dafa kafaɗarsa ta ce "Vi, ka yi haƙuri dan Allah, kar ka sanya damuwa da yawa a ranka, kamar yadda wasu daga cikin mutane ba sa girbar tarin alkhairin da suka shuka, suke komawa ga Allah, su tarar da sakamakon su a can, haka wasu daga cikin waɗanda suke aikata ɓarna, ba sa girbar abin da suka shuka, sai a gaban Allah. Wata shari'ar sai a lahira ai" Viper ya jinjina kai ya ce "Haka ne" Alhaji mu'azzam ya ce "Haka ne zancenki, ni kaina nayi iya ƙoƙarina, na ga Indabo an hukunta shi, amma abu ya gagara, shiyasa na haƙura na zuba wa sarautar Allah ido, ka yi haƙuri Viper, mun san an cutar da kai, amma ci gaba da jayayya da dagewa lallai sai ka ga bayan indabo, zai ƙara complicating abubuwa ne kawai, lokaci ya yi da yakamata ka yi relaxing, ka huta ka nutsu ka yi enjoying life ɗin ka. Indabo kuma ka zuba ido, hakkin abubuwan da ya aikata, ba zai taɓa barinsa ya rayu cikin aminci da kwanciyar hankali ba, ko a yanzu ka kafa tarihi, kuma rayuwar gidan indabo ta watse, dan haka ka yi haƙuri" Viper ya jinjina kai, "Yauwwa, Ubangiji Allah ya yi maka jagora, ya kawo maka ci gaba na ban mamaki" Suka amsa da Amin. Viper ya kalli Alhaji mu'azzam ya ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya saka da alkhairi" "Bakomai kar ka damu" Ya sake kallon Alhaji mu'azzam ya ce "Ka tafi da ita wurin hafsa dan Allah, ta huta ta kwana a can idan ban takura maka ba" Alhaji mu'azzam ya ce "Wane irin takura kuma, ba takura ai dama yakamata ta kawo mana ziyara" Nabila kuwa ta ce "Yaya za ayi na tafi na bar ka, wa zai yi jinyarka?" Viper ya ce "Kar ki damu, babu abin da zan nema na rasa in sha Allah, ana kula da ni" "Ni gaskiya ko na tafi ba zan iya nutsuwa ba, hankalina ba zai kwanta ba, ka bari idan ka samu lafiya na je gidan nata" Ya tsuke fuska ya ce "Zaki fara ko? Ba zan ce ayi abu ba ki yi, sai kin yi gardama ko?" Ta marairaice ta ce "Dan Allah vi, wallahi hankalina.... Kallon da ya yi mata ne ya sanya ta yin shiru, idonta na cika da hawaye. Haka tana ji tana gani, ta tafi ta bar shi. Gidan hafsa gida ne haɗaɗɗe mai matuƙar kyawun gaske, Hafsa na ganin Nabila ta rungumeta tana murna. Ta kalli Kankarofi ta ce "Yallaɓai, ina ka tsinto mini ita, ko ta biyo maigidan ne ban sani ba, ba ta gaya mini ba?" Ya ce "Ina fa, wani case ɗin ya kuma tasowa" nan ya gaya mata abin da ya faru. Jiki a sanyaye hafsa ta ce "Kai, Allah ya isa tsakaninmu da wannan azzalumin mutumin, Allah ya shiga tsakaninmu da shi, amma ya jikin Yaya Al'amin ɗin?" Alhaji mu'azzam ya ce "Jikinsa da sauƙi, duk da yana da ƙarfin hali, amma an harbe shi a kafaɗa" Cikin tausayawa ta kalli Nabila ta ce "Ki yi haƙuri kin ji ƙanwata, in sha Allah zai samu lafiya" Nabila kuwa ɗan kukan da take maƙalewa ya ƙwace mata, Hafsa ta din ga rarrashinta, ta kaita ɗaki ta yi wanka ta bata kaya ta saka. Ta ci gaba da rarrashinta, daga nan kuma suka shiga hira, a lokacin Nabila take bata labarin wasu abubuwan, tun daga haɗuwarta da Viper. "Ya sha wahala sosai da sosai, ina matuƙar jin tausayinsa, daga wannan sai wannan" Hafsa ta ce "Kin san da haka amma ki ka din ga bori wai ba kya son aurenku" "Ina da dalilina mai ƙarfi na yin haka, amma koma dai menene ya riga ya wuce, Ubangiji Allah ya sassauta masa" Hafsa ta amsa da Amin tare da ci gaba da rarrashinta. A ranar aka fitar da sanarwar cewa, Viper ba ɗan ta'adda bane ba, domin yana aiki ne da rundunar tsaro ta ƙasa, kuma harbi ya yi shi ne a kan ƙa'ida, babu daɗewa za su fitar da rahoton ainihin abin da ya faru. Walid ya dawo daga kasuwa, bai samu dawowa gida da wuri ba, saboda ayyuka da suka yi yawa, kuma sai da ya biya wurin liti suka ɗan yi hira, suka zauna a joint tare, daga nan ya taho gida. Ya sha shagwaɓa da tuhumar dalilin daɗewarsa daga wurin amarya Shahida, kafin daga bisani ta gabatar masa da abincin sa na dare. Wayar Viper ya kira, bayan ya gama, ya ɗaga amma bai ce komai ba. "Mai zamani, wai ina ka shiga ne kwana biyu bana samun wayarka, hankalina ya tashi sosai, liti ma ya ce mini ba ya samunka" Ya sauke numfashi ya ce "Ina lafiya" "Mai zamani" "Mai laya" Walid ya ce "Akwai matsala, menene yake faruwa?" Viper ya ce "Nothing much, kar ka damu ya ƙanwata" "Da akwai matsala, kuma ba ƙarama ba ce ba, kamar yadda ka ke faɗa, meyake faruwa?" "Koma da akwai matsala, ba gashi kana ji na ba, babu wata matsala ba abin damuwa ba ne ba" "Ka san ba abu ne mai wahala na yi sammako na taho Abujan nan ba, ka gaya mini menene?" Walid ya yi maganar a hasale. "Easy maza, harbina aka yi, amma ina samun sauƙi, kar ka ɗaga hankalinka" Walid ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, kuma ka kasa gaya mini, ka ke cewa ba abun damuwa bane ba" "Eh, bana son ɗaga muku hankali ne, dan Allah kar ka gaya wa kowa, kuma kar ka ce zaka zo, ba ni tabbacin hanya tana da kyau" "Anya zan iya haƙuri ban zo ba, Viper kar ka ɓoye mini wani abu" "Kai dalla ware ina gaya maka magana kana ja, zan saka maka ƙarfe ka kuma ƙoƙarin ƙaryatani, ja jiki dalla, mai laya" Walid bai san lokacin da dariya ta suɓuce masa ba ya ce "Na kiyayi mai zamani, tuba nake ka san ɗaukar ƙarfenka ba duk kai ba, na sallama tuba nake, Allah ya ƙara lafiya, ya ja zamaninka mai dogon zamani" Viper ma yayi murmushi ya ce "Sai da kai na wajena, ka gaida mini ƙanwata" "Zata ji in sha Allah" suka yi sallama ya ajiye wayar yana murmushi. Ba a awa uku, sai Nabila ta kira Viper, ta tambaye shi yaya jikinsa. Har ga Allah ta so ta kwana tare da shi, amma ya koreta ya saka aka tafi da ita. Da kyar ta iya cin abincin dare, Walid ya kirata, yana yi mata mitar, meyasa ba ta gaya masa abin da ya samu Viper ba, ta gaya masa ba ta sani ba sai daren jiya, ita ma yau ta zo ta ganshi, amma ta tabattar masa da jikinsa da sauƙi. Ƙarfe uku da rabi, alarm ɗinta ya buga, ta tashi zaune, haka kurum sai ta kira lambar Viper, gani take yi kamar wani abu zai same shi, ga mamakinta kawai ta ji ya ɗaga. "Vi" "Mmm" "Baka yi bacci ba idonka biyu?" Ya ce "Mmm" "To meyasa?" "Ciwo" ya bata amsa muryarsa ƙasa-ƙasa. Ta miƙe tsaye ta ce "Ka gani ko, da ka bari na kwana tare da kai, atleast ina kusa da kai, na taimaka maka da wani abun, wurin harbin ne yake yi maka ciwo?" "Mmm" "Sannu Vi, Allah ya baka lafiya ya sanya kaffara ne" tayi maganar tana kuka. "Abla, stop crying, babu zafi sosai kawai na kasa bacci ne" "A'a da zafi mana, ina jin zafin a zuciyata" Shiru ya yi yana tuna lokacin da jauhar take yi masa magiyar, ya daina zuwa in da za a cutar da shi, saboda ita take jin zafin a zuciyarta. "Ki na ji na?" "Eh" "Ki kwantar da hankalinki, ki daina kuka Please, idan ba haka ba, zan ba da umarni a hana ki ganina, har sai na warke" "Yi haƙuri na daina" "To shikenan, ki yi bacci mai daɗi"ya katse wayar. ***** Bunkure ta din ga zuba ido, ta ga ta ina za ayi belinta, domin kuwa ba wuri ɗaya aka kaita da su Indabo ba, ita Kano aka yo da ita, domin ta fara Fuskantar tuhuma ta farko, da ake yi mata a kano, amma shiru babu alamar za ayi belinta, jami'an tsaro suka tabbatar mata da cewa a gaban kotu za a gurfanar da ita. Abokan aikinta da suka kai mata ziyara, suka tabattar mata da cewa an bayar da belin indabo, daga majiya mai ƙarfi, kuma ba a sanar da cewa an kama shi ba, ita ce kaɗai labarin kamata ya cika media. Abin ya ɗaure mata kai sosai da sosai, sai dai ta yi masa uzuri, ta ƙara masa kwanaki, ko zai waiwayota ya sanya a bayar da belinta. Washegari da sassafe Nabila da Hafsa tare da Alhaji Mu'azzam, suka tafi wurin Viper. Ko da su ka je, Nabila da Hafsa ne suka shiga, shi kuma Alhaji mu'azzam ya tsaya a wani office. Suka tarar an buɗe wurin raunin Viper ana dressing. Da sauri Nabila ta ƙarasa, ta zauna ta gefen sa tana yi masa sannu, cikin kulawa da tausayawa. Ya langaɓo kansa jikinta ya ce "Washh da zafi" sai ta sake rikicewa cikin tausayawa ta ce "Sannu Vi, dan Allah doctor ka yi masa a hankali" Likitan ya ce "Ba wani zafi, tun ɗazu nake durje ciwon, bai ce da zafi ba sai da ki ka zo" Viper ya ce "Abla zafi, da zafi yake yi mini" Hafsa kuwa riƙe baki tayi, tana kallon ikon Allah, da wani ne ya gaya mata zata ce an zabga mata ƙarya ne, kodayeke ba abin mamaki bane, ko a baya Jauhar yana sakin jiki da ita. Nabila kuwa ta sake rikicewa ta ce "Dan Allah ciwon nan ya wanku haka a ƙyale shi" Likitan kasancewar sa, bahaushe ne ya ce "Sai dai ya yi kukan jini, sai na cuɗe shi sosai" Marairaicewa Nabila ta yi kawai ta saka kuka, domin ramin da taga wurin harbin yayi, kuma a haka likitan yana cewa wai bashi da ƙan jiki, wurin ya ciko. "Ke da wasa nake yi fa, ba wani zafi kawai ina son in ga kina kula da ni ne" "You are just pretending, amma na san da zafi" Yayi murmushi ya ce "Idan muka koma gida, ke zaki ci gaba da yi mini dressing ɗin fa" Ta girgiza kai ta ce "Ba zan iya ba, kuka zan ta yi" Viper yana kallo Hafsa ta silale ta bar ɗakin, bayan ta ajiye kayan abincin hannunta. "Zafin shigar bullet ɗin, bai kai zafin ƙiyayyar da ki ka nuna mini ba, ya taɓa zuciyata sosai" Ta marairaice ta ce "Am sorry Vi, dan Allah ka daina tunawa mana" dai-dai lokacin likitan ya kammala nananɗe masa hannun ya ce "Gashi nan maza ki haɗiye shi madam" Nabila ta yi murmushi, sai a lokacin ta farga Hafsa ba ta nan, ta ce "Kai, tare fa muka shigo da hafsa, tana ina?" "Ta fita tun ɗazu, taga abin naki ba na ƙare bane ba" yayi maganar yana janyota jikinsa. Ta tura baki ta ce "Ni da suka din ga soyayya a gabana ya na yi, ko kunyata ba sa ji" "Mhmm su su na can su na soyayya, ke ki na takaicin an yi miki auren dole" Tashi ta yi daga jikinsa, saboda da lafiyayyen hannun, yake ƙoƙarin fara lalubeta, ta ce "Bari na baka abinci ka karya, yaya ka kwana da jikin?" "Jikina Alhamdilillah, yau zan fita ma na zagaya, na ji sauƙi sosai da sosai" Tana cikin haɗa masa breakfast, Alhaji mu'azzam ya shigo tare da Hafsa. Suka duba jikin Viper, Alhaji mu'azzam ya ce "Minista zai zo dubaka anjima in sha Allah" Viper ya ce "Ni ɗin?" "Eh kai fa" ya kalli Nabila ta kalle shi. Ta ce "Yallaɓai, Viper ministan tsaro zai zo ya duba?" Alhaji mu'azzam ya ce "Ni ma ba ƙaramin ministan bane, ai komai sila ne Nabila, kuma idan Allah ya yi niyyar yi maka wani abu, ko da sai ka sha baƙar wahala, kan ka same shi, sai ya baka abin nan. Da gudunmawarsa ɗari bisa ɗari na din ga gudanar da wasu abubuwan, na taimaka wa rayuwarka. In sha Allah kukan da ki ke yi na sha wahala, zai zame masa alkhairi, dan na yi masa bayaninsa sosai da sosai, kuma mussaman saboda kai ya kira ya ce lallai ayi bincike a wanke ka, dan haka ka kwantar da hankalinka in sha Allah babu abin da zai faru da kai sai alkhairi, wahalar da ka sha, ba zata taɓa tafiya a banza ba in sha Allah" Shi dai Viper jin abin yake kamar ba gaske ba, bayan sun gama, Alhaji mu'azzam suka tafi, suka bar Nabila, da zummar da yamma za a zo a ɗauke ta. Viper zuciyarsa ya din ga kaiwa nesa, kasancewar sa da daga shi Nabila, saiti yana neman ya ƙwace masa, duk da a da yana iya sarrafa kansa yadda yakamata. Ya ja ta suka fita yawo, idan suka haɗu da na ƙasa da shi, su sara masa, idan na sama da shi ne, ya sara musu. Duk da gargaɗin da Viper ya yi wa Walid, amma sai da ya gaya wa Liti, abin da yake faruwa, ƙarshe sai da suka yi video call da shi, sannan hankalinsu ya kwanta. Sai da aka kwana huɗu, sannan Alhaji mu'azzam ya zo tare da ministan tsaro, kamar yadda ya sanar da Viper zai zo duba shi, ba kuma shikaɗai ba, har da babban hafsin soja na ƙasa, da wasu daga manyan shugabannin rukunin sojoji masu irin aiki irin na Viper. Yana zaune a kan gadonsa, Nabila na kan kujera, suka shigo, ta tashi tsaye tana kallon su, sai da ta gansu tare da Alhaji mu'zzam, sannan ta ɗan nutsu. Yana zuwa ya miƙa wa Viper hannu, sai da ya ɗan yi jimm, sannan ya miƙa masa suka gaisa. "Finally, yau gani ga Viper, ya ci sunansa Viper, yayi kalar mazaje" yayi maganar yana murmushi. Ɗaya daga sojojin ya ce "He's very intelligent, and hardworking man, da taimakon team ɗin sa, mun daƙila hare-hare masu yawa, yana taimakawa rundunar tsaro sosai da sosai" Ya jinjina kai ya ce "Na ji daɗi sosai da sosai, duk da ta wani fannin mun aikata laifi, na cireka daga prison, aka yi maka horo na musamman, amma da wata ɓarnar gara wata, na ji labarin duk abin da ya sameka, hakan ya sanya na ƙara samun ƙwarin gwiwar saka hannu a taimaki rayuwar ka, duk da ka bamu wahala da farko, dan sai da na ce, idan zaka bayar da matsala gara a kasheka, amma Kankarofi ya dage, ya ce a bika a hankali. Ina jimanta abin da ya same ka, Allah ya baka lafiya, sannan zan san abin da zamu yi maka, mu ƙara ɗaga darajarka a gidan soja, you are brave man Al'amin, the entire nation is proud of you. Ka yi abin da ya dace, sauran kuma ko su hukunta masu laifin, ko su bar su, wannan kuma su da Allah ne, get well soon my man" yayi maganar yana dukan kafaɗar Viper. Alhaji mu'azzam ya ce "Ga kuma madam ɗin sa fa, his lioness wife, barrister Nabila, yarinyar da nake baka labari, mutuniyar Naja'atu Bunkure" "Kai, to ai na ganta yarinya ƙarama" "Eh yarinya mai kasada ba, su suka assasa lallai ayi wa Indabo kiranye, amma aka daƙile su, ai nan Abuja zata dawo, ku nema mata gurbi gaskiya, a din ga matsawa matasanmu, suna gwada mana tasu baiwar, hatta cheif judge ya san da ita, amma ita ba ta sani ba" Shugaban hafsin Sojojin ya ce "Tabbas ƙasarmu Nigeria tana da nagarttun matasa, wanda za a basu dama, zasu kawo gayar a abubuwa da yawa. Kamar history ɗin Viper da na duba, da tun tasowarsa, ya samu abin da ya dace, to da tabbas a irin ƙwaƙwalwarsa, da wataƙila shi ne a kujerata, ya zama matashi mafi ƙarancin shekaru da ya riƙe rundunar tsaro ta Nigeria, na yaba da basirarsa nesa ba kusa ba" Nabila ta ji daɗin yabon da Viper ya samu, bakinta har kunne, bayan fitarsu ba ta san lokacin da ta rungume shi ba, tana ta yi wa Allah godiya. Ta ce "Ka ga abin da na gaya maka ko? Dama lokuta da dama, Allah yana jarraba bawansa, kafin ya yi masa wata baiwa, Alhamdilillah ala kulli halin, Allah ya ƙara ɗaukaka Vi" Murmushi kawai ya yi mata, shi dai baya fatan ace za ayi masa wani babban matsayi, saboda yana da 'yan adawa a cikin jami'an tsaron, gani suke kamar akwai wani fifiko na musamman da ake ba shi. Bayan tafiyar baƙin, shugaban sojojin yake cewa kankarofi, yana yi wa Nabila kallon sani, tana kama da wani tsohon ubnagidansa a sojoji, major Yusuf maitama. Kankarofi ya ce "Ai 'yar sa ce" Ya ce "In dai jarumta ce da taurin zuciya, ba ta yar a ƙasa ba" Minista ya ce yana son a saka sunan Viper, cikin sabbin naɗe-naɗen da za ayi na sojoji, a yi wa manyan ritire. Shugaban ɓangaren su Viper ya ce "Amma sir, lokaci bai yi ba ayi masa wannan muƙamin fa" "Eh a banza ma, ana saka waɗanda ba su cancanta ba, dan haka a saka mini sunansa, dan ya cancanta" ya ja bakinsa ya tsuke, domin kuwa kujerar da za a ɗora Viper, daga ita sai tasa. A daddafe Viper yayi kwana tara, ranar na goma ya ce a gidansa zai kwana, ya din ga zuwa dressing ɗin, ya gaji da zaman Asibiti. Nabila ma ta ji daɗin hakan, dan kuwa ta gaji da sintirin nan, babu wanda suka gayawa halin da ake ciki, a 'yan uwa, duk Major ya samu labari, ya kira Viper ya din ga faɗa a kan meyasa ba su faɗa ba, Nabila ta kaee shi, ta ce masa basa son tayar wa mutane hankali ne. Allah ya taimake su, an daƙile yaɗuwar labarin ƙaryar cewar Viper ɗan ta'adda ne. Nabila tana ta yi wa Viper santin gidan, ɗan ƙarami mai kyau, hafsa har gidan ta rakata, ta tayata suka yi 'yan gyare-gyare, komai akwai a gidan na furnitures da na buƙatu. Sai dai komai na maza ne, sai da hafsa ta tafi gida, ta aiko mata da wasu abubuwan. Nabila tana ta tsokanarsa, wai gidan gwauro. Ya kalleta ya ce "Gidan gwauro ko, zaki ga gidan gwauro, yau zan mayar da shi na magidanci" Sai kuma tayi ɗif, ta sha jinin jikinta. *GA MASU JIRAN DOCUMENT, ZA SU IYA PAYMENT YANZU, FEW PAGES YA RAGE, ONGOING PAGES NE 500 COMPLETE DOCUMENT KUMA 1K. VIA 0009450228 AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143 Ayshercool 08081012143 Ayshercool 08081012143 Wani irin miskilin murmushi yayi, tare da gyara zamansa a kan doguwar kujera. Nabila ta ɗan saki jikinta, duba da yadda haryanzu hannunsa da saura, bai gama warkewa ba, amma ya ci gaba da yi mata wani irin murmushi da shikaɗai ya san ma'anarsa, ƙarshe jikinta ya koma zauna tare da kwantar da kansa a jikinta. Suna yin sallar isha'i Nabila ta sulale daga parlour ta shiga ɗaya daga cikin bedrooms ɗin gidan, don ta ga al'amuran na Viper yau suna ƙoƙarin girmar tunaninta. Ajiyar zuciya ta sauke cikin mayar da numfashi tare da bin jikinta da ke ƙamshinsa da kallo, guntun murmushi ta yi ta shige toilet, bayan ta yi wanka ta ɗauro towel ta sanya hijjabi ta fito, ta ɗauko kayan da Hafsah ta aiko mata da su. Kayan turarurruka ne, masu ƙamshin gaske, da kayan wurin maman dr., Dan tana ɗagawa, taga sticker jikinsu. Kiran hafsa ta yi a waya, hafsa ta ɗaga tare da faɗin "Nabilatu, ya kawo miki kayan?" "Wannan kayan watsewar waye zai yi amfani da su?" "Ke mana, malama ki yi abin da ya dace please, a sha amarci lafiya" ta katse wayar tana murmushi. Nabila ta girgiza kai, ta ci gaba da dudduba kayan, kasancewar ba a shirye ta taho Abuja ba, hafsa duk ta haɗo mata kayan sakawa da na bacci. Humra kawai ta ɗauka saboda yadda ƙamshinta ya daki hancinta tun kafin ta buɗe murfin, ta ɗaga hijab ɗin ta shafe jikinta da ita tana lumshe ido saboda daɗin ƙamshin kamar ƙara shi ake, sassanya ƙamshi ne, mai ratsa zuciya. Lokaci ɗaya ɗakin ya buɗaɗe gabaɗaya da ƙamshin. Tana ɗaga ɓingilallun kayan baccin da Hafsan ta haɗo mata da su Viper ya turo ƙofa ya shigo, da sauri ta yi ƙasa da kayan cikin faɗuwar gaba tana ɓoyewa kamar mara gaskiya, a hanzarce ta  fara mayar wa cikin jakar da ta ciro su, a ranta tana faɗin. 'Wa zai saka wannan abun kamar matacin koko?.' Bai ce mata komai ba ya jingina a jikin ƙofa tare da zuba wa bayanta ido, kasa juyowa ta yi ta fuskance shi, saboda wata irin kunya da tsoron shi da suke ƙara cika mata zuciya. A hankali ya taka ya ƙarasa inda take ya tsugunna a daf da ita, yana jin yadda ƙamshinta yake ƙoƙarin zauta shi, lumshe idonsa ya yi cikin wata irin murya da ba ta san yana da ita ba ya ce. "Haka ake jinya da ma a tafi a bar mara lafiya shi kaɗai?" Kanta a ƙasa ta ce. "To ai na ga ka warke, kuma ni bacci nake ji, tun da na zo Abuja ban yi isashshen bacci ba." Shirun da ta ji bai kuma magana ba ya sa ta ɗaga kai ta kalle shi, wani irin kallo da ya burkita mata zuciya ta ga yana bin ta da shi wanda ya sa ta ji wani bakon al'amari a jikinta. Ƙoƙarin janye idonta ta yi amma ya hana ta, ta hanyar kama haɓarta ya ɗaga fuskarta tare da saka idanunsa da suka ƙanƙance a cikin nata. Ba za ta iya jure tasirin abubuwan da take gani daga idanunsa suna shiga cikin nata ba, hakan ya sa ta lumshe natan da sauri tare da ƙoƙarin ƙwace fuskarta. "Ina Ablata mai tsiwa ta tafi ne?" Ya faɗa yana ƙara matsar da fuskarsa daf da tata. A ruɗe ta janye jikinta baya, kamar za ta yi kuka ta ce. "Ban da lafiya ni fa, kuma na faɗa maka bacci nake ji, haba Vi." Guntun murmushi ya yi ya zauna da kyau a kusa da ita har jikinsu na gogar na juna, idanunsa akan ƙirjinta da ke ɗagawa saboda bugun da zuciyarta take yi mata ya ce. "Faɗa mini me kike tsoro ne? Ni ban gane firgicin duk na mene ne ba fa?" Baki ta tura masa cikin kunya ba ta ce komai ba. Ɗanyatsansa ya saka ya fara zagaye lip ɗinta da su, tsit ta yi ba ta hana shi ba sai ma lumshe ido da ta yi, a hankali ya kwantar da kanta akan kafaɗarsa mara ciwon, tare da saka hannu ya zagaye ƙugunta da shi. Bakinsa ya kai kunnenta kamar mai raɗa ya ce. "Uhmmm, ƙamshin nan daɗi, kamar na dawwama ina shaƙar shi." Ya ƙarashe maganar yana shinshina wuyanta ta jikin hijjabin. Da sauri ta ture shi ganin yana ƙoƙarin ɗaga hijab ɗin jikinta, ga shi babu komai a jikinta sai towel, shi ma tana ji ya kunce ɗazu, hijab ɗin ne kawai rufin asirinta ga shi yana ƙoƙarin bankaɗa mata shi. Kara naniƙar ta ya yi yana sassauke mata numfashi a fuska, gabaɗaya ya burkice mata kamar ba shi ba, ko son kallon fuskarsa ba ta yi saboda yadda idanunsa suka canza kala, ta lura kuma ƙamshin jikinta ne ya ƙara tunzura shi, ganin yana ƙoƙarin wuce gona da iri ta danne tarin tsoron da ke ranta don ta alamar sai ta haɗa da dabara za ta samu ta ƙwaci kanta, cikin kulawa ta ce. "Vi" "Uhmm.." Ya amsa mata a ƙasan maƙoshi. "Magungunanka fa, na san ba ka sha ba, kar lokaci ya ƙure." Bai ce komai ba ya zare jikinsa a hankali ya kwanta a kan carpet ɗin da suke kai yana mayar da numfashi, wani irin yanayi yake ji da zai iya cewa rabonsa da shi, tun lokacin babyn robarsa, yadda jikinta yake rawa ne kawai ya sa ya ƙyale ta. "Ka tashi mu je ka sha." Ta faɗa a shagwaɓe. Kallon ta ya yi, da sauri ta yi ƙasa da kanta. "Magani ba zai yi mini maganin abin da yake damuna ba, don haka yau ba zan sha magani ba, fanka nake so." Ya faɗa a sanyaye kamar wanda aka yiwa duka. Da mamaki ta ce. "Fanka kuma?" Gyaɗa mata kai ya yi tare da lumshe idonsa. "Ina jin zafi sosai." Ya faɗa ƙasa-ƙasa yana lumshe ido. Cikin rashin fahimta ta ce. "Wai wacce fanka kake magana ne, bayan ga A.C " "Taki kawai nake son sha, za ki ba ni?" Ya sake faɗa tare da ɗage mata gira. Ta jinjina masa kai cikin wasi-wasi, dan ba ta san meyake nufi ba. "Kin tabbatar Abla?" Ya ƙara tambayar ta. Ta ɗaga masa kai, kamar ƙadangaruwa. Tashi zaune ya yi yana ci gaba da bin ta da kallon da ba ta so ya ce. "Na gaji da ganin wannan abun, ina ta son na cire kuma kin hana ni, ki cire da kanki." Yayi maganar yana nuna mata hijjabin jikinta. Ƙara tukukuye shi a jikinta ta yi ta ce. "Ina ruwanka da abuna, don Allah ka koma ɗakinka ka bar ni na yi baccina." "Ni ko nake da ruwa da shi tunda ya hana ni rawar gaban hantsi. Ni yaushe ma ki ka fara saka hijjabi ne abla, haka ki ke yawonki fa da" Waro ido ta yi ta ce "Haba Vi, wannan shaidar zaka yi mini, wallahi ka san dama can ina saka hijjabi, idan ba dogwayen riguna ba, ina saka hijjabi. "To na ji, amma yanzu cire wannan" Ba ta kula shi ta miƙe da sauri tana riƙe towel ɗin ta nufi hanyar toilet, shi ma bai kuma magana ba ya tashi ya fice. Dafe ƙirji ta yi tana sakin ajiyar zuciya, tambayar kanta ta shiga yi anya kuwa wannan viper ɗin da ta sani ne? Gabaɗaya ya canza mata, kamar ba shi ne mai wannan muzuran da tsare gida ba, ga shi sai wani narke mata yake kamar wani jariri, kallon hannunta da ya dinga jagwalgwalawa ta yi tare da sakin murmushi, kamar har yanzu yana cikin nasa haka take ji. "I love you so much my Vi."  Ta furta a hankali, ashe duk wannan maziyar ya iya kalamai da tausasawa haka? Ta faɗa tana ɗora hannun a kan ƙirjinta tare da lumshe ido, tana jin yadda zuciyarta take bugawa. Gudun kar ya ƙara dawowa ya same ta a haka ya sa ta fita ta shirya cikin wata doguwar riga a cikin kayan  mara nauyi, don ba za ta iya saka ɗaya rigar ba. A zaman jinyar shi da ta yi sun ƙara shaƙuwa sosai, kuma ta rage jin kunyar shi, amma a yau da suka dawo gida za su kwana su kaɗai sai komai ya dawo mata sabo fil, musamman yadda yake ta rawar ƙafa a kanta, ta san mai ƙwatar ta sai Allah, dan ta fara ganin saɓanin abin da take tunani. Har za ta kwanta sai ta fasa ta zura hijabi ta fita parlour, ta san bai sha magungunansa ba, kuma idan ba ita ta ba shi ba bai zama lallai ya sha ba, dan tun da Allah ya sa ya daina shan ƙwayoyi, yake adawa da su, ko da kuwa ba shi da lafiya ne, ko warin magani ba ya so. Tana fita shi ma yana fitowa daga ɗakin da yake facing nata, da sauri ta juya masa baya ganin daga shi sai gajeren wando ko singlet babu a jikinsa. Jin takunsa yana nufo ta ya sa ta yi ƙoƙarin komawa ɗakin a hanzarce, amma haƙanta bai cimma ruwa ba don cak ta ji ya ɗaga ta bayan ya damƙe ta. A ɗimauce tana zaro ido ta ce. "Na shiga uku! Don Allah ka yi haƙuri ka sauke ni, ka ga ba ka da lafiya kar ka fama ciwonka." Bai ce mata komai ba ya fara tafiya, ba ta da zaɓi wanda ya wuce ta riƙe shi don kar ta faɗi, hannunta ta sakala ta wuyansa ta zagaye bayansa da shi ta ƙanƙame shi, kamar bai ɗauki komai ba. A tsakiyar parlourn ya zaunar da su tare da faɗin. "Ana so ana kaiwa kasuwa." Ɓata fuska ta yi tare da kawar da kanta ta ce. "Please Vi ka je ka saka riga kar sanyi ya shige ka." Karan hancinta ya ja tare da faɗin. "Na faɗa miki ni zafi nake ji, kin ƙi mun maganinsa ke kuma." A shagwaɓe ta ce. "To ai ni ban san wane irin zafi ne wannan ba, ga sanyin A.C amma idan kana so sai na yi maka firfita har ka yi bacci, ka yarda?" Gyaɗa mata kai ya yi tare da janyo ledar da ke gabansa, har lokacin tana jikinsa ya ƙi barin ta, ta tashi kamar yadda take ta ƙoƙari. Tun kafin ya buɗe ƙamshin ya daki hancinta, ya ware ya ɗauko yankan naman kazar ɗaya ya kai bakinta tare da faɗin. "Yau da kaina zan ba ki, tunda wancan karon ƙin ci ki ka yi, saboda ba kya so na, yanzu kuwa tun da zan kwana ina shan iskar fifitar da za ki mun, sai na baki da kaina." Murmushi ta yi cikin mamakin sabuwar lallaɓawar da yake yi mata ta buɗe bakin ya zira mata. Shi ya yi ta ba ta a baki har ta ƙoshi, da ta ce ya ci sai ya ƙi ya ce shi ya ƙoshi, da ma tata ce ya siyo mata. Wani kallo ta yi masa ta ce. "Yaushe ma ka fita ka siyo?" Ya ce. "Order na yi aka kawo har gida." Ba ta kuma magana ba ta tattara ragowar ta kai kitchen, ta dawo ta gyara gurin. Har lokacin yana zaune yana ta aikin kallon ta tana ta fama da hijabi, kamar mai takaba. So take ta gudu ɗaki ta bar shi amma zuciyarta ta ƙi yarda da hakan, musamman a halin da yake ciki na rashin lafiya. Kusa da shi ya nuna mata ya ce ta zauna su yi magana, ba ta yi musu ba ta zauna, tare da tattara hankalinta wuri guda. "Wai wannan hijabin na mene kamar wata mai takaba?" Ido ta juya masa ta ce. "Sanyi nake ji ne." "Ni ina jin zafi ke kuma kina jin sanyi, sammun naki na sammiki nawa sai duk mu daina ji." Ya yi maganar tare da cire hijabin ya ajiye a gefe. Dogon gashinta ya bayyana kasancewar babu dankwali a kanta. Idanunsa akan inda ya fi yawan takurawa da kallo a jikinta ya kai hannunsa ya fara shafa gashin a hankali, yadda gashin jauhar yake, mara yawa sai tsayi haka na Nabila yake, kuma ba baƙi ne ƙirin ba. Da sauri ta juya masa baya ta ce. "Ka daina ba ni kunya don Allah." Ya ce "Ni fa ba wannan Nabilar na sani ba, a dawo mini da ta bayana mara tsoro da kunya, mai kallon cikin idanuwana, tana gasa mini magana yadda ta ga dama." Ya faɗa yana leƙa fuskarta. Cikin rigima ta ce. "Kana nufin ban da kunya kenan ni mara kunya ce?" Hannunsa ya zura a inda ba ta taɓa tsammani ba ya ce. "Mara kunyar dai nake son ki zama." Cikin ƙunƙuni na ce. "Kamar yadda ka zama ba." "Oush!" Ya faɗa yana yarfe hannuwa.  "Mene ne? Me ya faru?" Kafaɗarsa ya nuna mata bai ce komai ba. A ruɗe ta ce. "Ciwo take maka? Ko ka fama ciwon ne?" Yamutsa fuska ya yi ya ce. "Har cikin ma duk suna mun ciwo." Yayi maganar yana nuna side ɗin cikin sa na dama. Ba ta san lokacin da ta janyo shi jikinta ta fara shafa fatar bayansa cikin rarrashi ba, kamar za ta yi kuka ta ce. "Sannu, ko mu koma asibitin ne? Dama fa baka gama samun sauƙi ba ka ce, sai mun dawo gida" Girgiza mata kai ya yi yana ƙara shigewa jikinta. Cikin kulawa da tausayawa ta shafa kansa ta ce. "Bari na ɗauko magungunan ka sha to, sai mu je ka kwanta." Kamar ƙwai haka ta dinga lallaɓa shi, shi kuma yana ƙara narkewa kamar gaske, ya ce mata nan da zafi can yana yi masa ciwo, har da hawayenta saboda tausayin shi. Tare suka koma ɗakinta yana manne da ita, ta buɗe jakarta, ta ɗaukko ledar magungunan, ta din ga bashi ɗaya bayan ɗaya yana sha yana yamutsa fuska, ta rage haske ta lulluɓa masa bargon da yake kan gadon. Sai sannu take yi masa duk ta ruɗa kanta, ko kadan tunaninta bai kawo wayo yake yi mata ba, saboda duk lokacin da aka buɗe raunin za ayi masa dressing sai ta tausaya masa, saboda ramin da wurin yayi. Sai da ta gama raɓe-raɓenta, ta din ga kai komo tsakanin ɗakin da falo, sai da tayi tunanin ya yi bacci, sannan taje ta raɓa ta kwanta, kamar mai hawa kan wuta, cike da matsanancin tsoro. Shikam idonsa biyu, sai da ya tabbatar ta saki jikinta sosai yadda yake so sannan ya fara gudanar da ƙudurinsa. A firgice ta janye jikinta daga nasa, cikin rawar murya ta ce. "Vi rashin lafiyar kenan? Kana buƙatar bacci, ka kwanta ka yi Please." Ƙara janyo ta ya yi cikin wata irin murya ya ce. "Ni fa na warke, taki rashin lafiyar kawai nake yi." A tsorace na ce. "To ni ban da lafiyar ka ƙyale ni." "A'a Abla, kar mu yi haka da ke, kar ki yi mini haka, kwana talatin da wani abu da aurenmu, kar mu yi haka da ke please" Cikin rauni da tsoro ta ce "Ni dai a'a bana so." Ta faɗa cikin kuka, don sosai wani irin tsoro yake ƙara lulluɓe ta. Tsayawa ya yi da abin da yake ya mayar da bakinsa kan kunnenta ya shiga hura mata iska, a hankali ta ji ta fara samun nutsuwa, ajiyar zuciya ta sauke ta koma hannunsa ta riƙe. Jauhar ce ta shiga kai komo a cikin kwanyarsa, baiwar Allah babu sawa babu fitarwa, babu gardamar tsiya kamar Nabila. "Abla" ya kira sunanta a hankali. "Na'am" "Amma ina alkawarin firfitar?" Ta ce"Yana nan, sai ka yi bacci zan yi maka." "Ba zan iya baccin ba ai" Juyawa ta yi suna kallon juna ta ce. "Wai wacce irin iska ce wannan, ni fa kana ta sa ni a duhu." Yana shafa gefen wuyanta ya ce. "Shi yasa nake so na fito da ke haske amma kin ƙi. "Vi" "Mmm" "Dan Allah ka yi haƙuri, ka ga ni marainiya ce" Ya ce "Menene haɗin aurena da maraicinki, nima marayan ne ai, sai fa na dangana da birnin tarayya" "Wace birnin tarayyar kuma?" Duk yadda ta so ƙwace kanta amma ta kasa, bisa tilas ta haƙura ta bar shi ya yi yadda yake so. Sai dai jin abun nasa na gaske ne ya sa ta dawo hayyacinta ta saka masa kuka tare da doguwar magiya kamar wanda zai zari ranta. Fuskarta da ta yi kaca-kaca da hawaye ya ƙura wa ido ta ɗan gutun hasken da ya rage a ɗakin yana jinjina taurin kai da tarin rigimarta, Jauhar ɗinsa mai sauƙin kai ce ta faɗo masa a rai, salihar baiwa kenan da sauri ya kawar da tunaninta, saboda alƙawarin da ya daukar wa kansa a wannan fagen ba zai taɓa yi wa Nabila maganarta ko ya yabe ta ba, a karan kansa ya ji duk da ƴar'uwarta ce amma ba za ta taɓa jin daɗi ba idan ya aikata hakan. Ba ya kuma so ta dinga jin haushin ta ko ta dinga kishinta kamar yadda ta ce masa yana sakawa ta ji a ranta. Amma da tabbas sai ya furta, ya yabawa yar madara. Duk iya ƙoƙarinsa na ganin ya riƙe kansa amma ya kasa, juriyar da ya yi shekaru yana yi ya kasa yin ta a dare ɗaya, sosai yake da buƙatar iskar da ya yi shekaru bai shaƙe ta ba. Sai da ya samu ɗin kuwa a daren ya samu sukuni, abin ya zo wa uwar gayyar a bazata. Ƙarshen gadon ta koma tana sheshaheƙar kuka tare da takure kanta guri ɗaya, shiru ya yi yana sauraren ta, bai yi yunƙurin rarrashin ta ba. Yadda ya tsallake Jauhar, bayan ya gama abin da Allah ya nufe shi da yi, saboda wata banzar poster indabo, Walid ya tafi neman magana, sai wani takaici ya mamaye zuciyar sa. Wai yau shi ne zai je shimfiɗar aurensa, ya ɗauki wanka ya sha turare. Wanda lokacin 'yar madara, wata ran da ƙaurin hayaƙinsa da komai idan ya dawo daga gantalinsa, komai dare wataran ma a buge, haka zai haye mata gado yana basarwa, shi a yi abin da yake so kawai. Daga baya sai ta dinga zama sai ta jira shi ya gama yawon ya dawo, ta lallaɓa shi cikin hikima, ta ce ita zai yi wa wankan, tun da ita ta saba wanka ba yau ba gobe kamar macen kunkuru kamar yadda yake faɗa. Da haka zata lallaɓa shi, su yi brush ayi wanka a shafa turare, daga nan idan tana da wani ɗan abin kusa da bakan ta bashi, ba ta taɓa yi masa magana ba, a hankali kuma ya gane yake jin daɗin hakan, ya zamana ko ba ta saka shi ba, zai yi abin sa ya shafa turare sannan ya zo in da take. Duk ranar da ta hana shi shan wani abu, ya je ya sha, sai ta sunsuna bakinsa, idan ta ji ƙauri, ranar ba zata saurare shi ba, sai dai yayi raragefensa ya gama. Jauhar ita ta mayar da shi ɗan gayu. Kukan Abla ne ya dawo da shi hayyacinsa, da ta shafe lokaci tana yi, ba tare da ta gaji ba. Ya mirgina kusa da ita ya yi ƙasa da bargon da ta lulluɓa har kanta. Cikin wani irin nishaɗi da ya cika masa zuciya haɗe da alhini ya ce. "Ablan Vi." Yadda ya yi maganar ya sa ta hadiye sauran kukan nata na zallar shagwaɓa ba tare da ta shirya ba. "Kukan ya isa haka idan kuma ba ki gaji ba to." Ya faɗa yana kwantar da kanta a kan ƙirjinsa, tare da bubbuga bayanta cikin rarrashi. Baki ta tura tare da ƙara shigewa jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, rarrashin take buƙata da ma. Tarairaya da kulawa kala-kala ya dinga nuna mata a daren tare da wata irin soyayya mai tsayawa a rai da wuyar mantawa, ita kuma ta dinga yi masa taɓara iri-iri. Bayan sun yi wanka ta koma bacci, shi kuma ya jima ya kasa baccin, ya din ga jin tamkar ya aikata wani zunubi mai nauyin gaske, yau shi ne da wata macen daban, ba 'yar madararsa ba. Duk zalama da ƙulafucin namiji da mace sama da ɗaya, bai taɓa jin haɗa jauhar da wata mace ba, amma Nabila wani sashi ce na jauhar, shiyasa ya bata wani gurbi a zuciyarsa, son Nabila son Jauhar ne, duk da ba ta raye. Tabbas ya san ban da Nabila ya aura, babu wata mace da zata iya zama da shi, a hakan ma ya san Nabila na matuƙar ƙoƙarin yaƙi da zuciyarta a kan Jauhar, shi dai duk wanda zai zauna da shi, to dole ya so Jauhar, ko su raba gari, haryanzu babu mace mafi ƙololuwar daraja a ransa bayan mahaifiyarsa sai jauhar, ko mahaifiyarsa, ba ta yi masa tarbiyyar da jauhar ta yi masa ba. A hankali ya furta "I miss you 'yar madara, may your gentle soul, rest in jannatul firdausi, may Allah subhanahu wata'ala grant you a highest rank in Janna" ya furta a hankali yana dafe saitin zuciyarsa, kamar yadda ya kan faru mafi yawan lokuta idan har ya tuna ta. Ganin ya kasa baccin, ya sanya ya tashi ya sake ɗauro alwala ya koma ɗaya ɗakin ya tayar da salla. Ya daɗe a sujuda, kawai yana nema mata gafarar Allah da rahamarsa, bai gushe ba idanunsa na zubar da hawaye, alkhairanta, na ci gaba da kai komo a cikin zuciyarsa. Sai da ya idar ya gabatar da sauran addu'oi, na neman tsari, da fatan zaman lafiya da kwanciyar hankali a musayar da Allah ya yi masa. Ya idar yayi shiru a kan dardumar, yana tunanin Jauhar kamar wata walƙiya ce, ko flashing da ta shigo rayuwarsa, dan kawai ta haska masa wasu abubuwa ta ɓace. Ya daɗe a zaune, sannan ya tashi ya koma ɗaki ya kwanta. Sai daf da Asuba bacci ya ɗauke shi, mafarki yayi gashi zaune a falo, Nabila na kujerar da take facing ɗin sa, suna ta hira cikin nishaɗi, sai ga Jauhar ta shigo, tana ta ƙamshin turaren da duk in da ya ji shi, sai ya yi tunanin zai ganta. Ta zuba musu ruwa a kofuna, ta zauna a kusa da Nabila, tana kallon yadda Nabila ke magana cikin nishaɗi. Murmushi take yi tana kallon Nabila, shi kuma yayi shiru yana bin Jauhar da kallo. Da alama Nabila ba ta ganin Jauhar, amma jauhar sai kallon Nabilan take tana murmushi, alamar tana jin daɗin yadda Nabila ke cikin fara'a. Viper take nuna wa Nabila tana murmushi. "Vi an kusa idar da salla fa" muryar Nabila ta tashe shi. A gida ya yi sallar asuba saboda ya makara, ita kuwa da ƙyar ya samu ta tashi ta yi sallar ta koma bacci. Shi ma baccin yayi, saboda jiya bai samu isasshen bacci ba. Naja'atu Bunkure kuwa tuni ta gurfana a gaban kuliya, bisa tarin zarge-zarge da ake yi mata. Ba ita kaɗai ba har da wasu daga cikin maƙarabbanta, da suka din ga gudanar da bunkure foundation. Ta musanta tuhume-tuhumen da aka yi mata, kuma lauyoyinta suka nemi a bayar da belinta, amma fafur alƙalin nan yaƙi, ya aike da ita gidan gyaran tarbiyya da kuma gyaran hali, wato gidan yari. Abin ya girmameta, tamkar zata zare ta haukace, wai yau ita ce, da ikonta da izzarta, aka aike da ita gidan kurku. Babu alamar Indabo zai zo ya fitar da ita, haka aka sakata a cikin masu laifi. Kamar mahaukaciya haka ta zama, tana tuna irin furucin da Nabila ta yi mata, ta tabbata sai da ta kaita ƙasa ta ga bayanta tukuna. Wani irin abu mai tsananin ɗaci ta haɗiye ta ce "Kuskure mafi girma da muni, da Indabo zai tafka, shi ne watsar da ni ya wanke kansa, ya zame ya bar ni. Wallahi muddin haka ta tabatta, ko kurkukun bayan duniya aka kai ni, sai na yi maganinsa, ni zan kawo ƙarshen sa, ƙarshe mai muni da ban tsoro, ni ce dai-dai da kai Indabo, mu zuba mu gani, sai dai ayi mutuwar kasko". Nabila ta riga Viper tashi, ta tafi ɗaya ɗakin, tayi wanka, dan kar ta dame shi da ɓuruntu ya tashi. Ta shiga kitchen ta duba abin da yake akwai na girki, ta fara ƙoƙarin sarrafawa, ta dawo falo ta cigaba da karkaɗe karkaɗe. Ta gama ta koma ɗaya bedroom ɗin, shi ma tana sake gyarawa, a nan ta ci karo da manyan frames, na hoton Viper da jauhar. A hankali ta ɗauki ɗaya daga ciki tana gogewa, babu wanda zai ce ba ita ce a jiki ba. Ta zubawa hoton ido, har ya shigo ba ta sani ba, sai daga baya ta razana jin motsi a bayanta. "Me ki ke yi da wannan hoton, ki kula kar ki fasa mini hoto" A sanyaye ta ce "Kallonta kawai nake yi" "Ki na sonta ne" da sauri ta kalleshi ta ce "So kai, wallahi har cikin zuciyata nake jin matsananciyar ƙaunarta, haryanzu ina jin zafi da ɗacin rashin saninta a rayuwata, da tare muka tashi babu lallai na zama masifaffiya ko?" Tayi maganar tana kallonsa. Dariya ya yi ya ce "Ai ke faɗa da tsiwa a jininki yake, ita kuma wannan haƙuri da kawaici ne a jininta, amma da ni da ita wa ki ka fi so?" Ta nuna masa hoton jauhar, ya saka hannu ya karɓi hoton ya ce "Nima ita na fi so" A sanyaye ta ce "Ko baka faɗa ba na sani, amma Vi dan Allah ba cin amana ne abin nan ba, haryanzu na kasa samun nutsuwa da auren nan, idan ina tuna wahalar da ta sha, sai na ga kamar na ci amanarta, da na fara sonka har na aureka" ta yi maganar idanunta na cika da hawaye. Ya rungumota jikinsa ya ce "Idan mafarkin da nayi gaskiya ne, to Jauhar tana murna da aurena da ke, kuma ta ji daɗin ganinki cikin farinciki" "Vi" "Mmm" "Na san ba zan iya zama jauhar ba, ba kuma zan taɓa kamota ba, ba zan taɓa haɗa matsayina da nata a wurnka ba, amma dan Allah ko babu yawa ka sama mini space a zuciyarka, kar maraicin yayi mini yawa" Wani irin tausayinta ya mamaye zuciyar sa ya ce "Ki na da naki space ɗin, ba zan bari maraici ya ci gaba da damunki ba, zan yi occupying spaces ɗin da suke cikin rayuwarki in sha Allah my abla" A hankali ta yi ajiyar zuciya ta ce "Na gode sosai da sosai Vi, Allah ya bamu zaman lafiya" Ya ce "Amin, yauwwa yakamata na yi comment akan fankar jiya, ita ma sanyinta ya yi, ba mai cutarwa ba ne ba" Ƙwacewa ta yi daga jikinsa ta ce "Kai ka san wata fanka, dama abin da ka ke nufi kenan, ka ke gaya mini zafi ka ke ji kwanaki, ko?" Ɗaga mata gira ɗaya ya yi yana murmushi. Ta ce "Bari na duba girki" Ya jinjina mata kai, ya sake ɗaga hoton Jauhar yana kallo, daga bisani ya mayar da shi in da yake. Suna karyawa yana tsokanarta, wai a ina ta iya girki har haka, shi ya zata ba ta iya komai ba, kawai ajebo ce. Dariya ta yi ta ce "Haba dai, boarding fa nayi har high institution, ace ban iya girki ba, girki yana cikin abubuwan da sukan sakani nishaɗi, da kuma kwalliya. Abba ne baya son make up, girki kuma sai na ga ina so nake yi, Abba ya hana sakani girki, idan ba ni na yi ra'ayi nayi ba" "Yar gatan Abba, gaskiya yana ji da ke sosai, dama har Jauhar shi ne ya riƙeta" "Shi kansa ya yi wannan nadamar ai" Ua jinjina kai ya ce "Maybe da shi ne ya riƙeta, da ba zan santa ba, Allah dai ya riga ya gama tsara komai, hakan ma mun gode masa" Wayarsa ta fara ringing, ya ɗaga ganin lambar Abbu. Suka gaisa, Abbu ya ce "Ina zamu yi, idan mun shigo Abuja?" "Wai zuwa za ku yi?" "Eh zuwa za mu yi, tun da kai ba ka ga ya dace ka sanar mana abin da ya faru ba" "Abbu ka yi haƙuri, na yi hakan ne dan kar na ɗaga muku hankali" "Koma menene gamu a hanya dai" "To bari na turo maka adress ɗin" Ya sauke wayar ya ce "Wai su Abbu su na hanya, ko wa ya gaya musu abin da ya faru, gashi an ta so su, next week na so mu koma gida fa" Nabila ta ce "Sai a ɗora girki, kafin su ƙaraso, amma sai an yi cefane" "Zaki iya kuwa, na ga jikin naki sai a hankali" Murmushi kawai ta yi ta tashi tsaye, ta ce "Zan iya mana" ***** Wani irin gumi ne yake tsatsafowa Indabo, cikin hasala ya ce "Wai wace irin Naja'atu kuma, ina ruwana da wata naja an kaita prison, iya ruwa fid da kai kawai a wannan gaɓar. Nan na ɓoyeta, na saka ake yi mata visa a ɓoye, ta bar ƙasar amma abun bai yiwu ba, wannan jarabben yaron maye, ya kawo mana farmaki, gashi gidan jaridar da aka bawa kwangilar yaɗa labarin, an maka su a kotu kuma tara za a caje su mai yawan gaske. Ko dai mu biya musu, ko su tona mana asiri. Gashi ba ni da tabbacin rundunar soja, za su ƙi faɗar ainihin abin da ya faru, dan su wanke Viper, gashi ministan tsaro ɗan uwan kankarofi ne, balle a sasanta komai yayi magana da su" "Ka kwantar da hankalinka, zuwa jibi war haka, ka bar ƙasar nan, kujerar sanatan ka haƙura, ace ka tafi neman lafiya, idan Allah ya sa komai ya lafa sai ka dawo, koma ka yi zamanka a can". Ayshercool 08081012143 *MASU JIRAN ƘARFE A WUTA COMPLETE DOCUMENT, ZA KU IYA PAYMENT A YANZU, A CIKIN SATIN NAN ZAI KAMMALA 1K VIA 0009450228 AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143 Yakice gumi Indabo ya yi, yana jinjina kai cike da gamsuwa. Zakiyya kuwa, hankalinta ya kwanta bayan ganin hafsa ta koma gidan Alhaji mu'azzam, babu irin huɗubar tsiyar da ba ta yi mata ba kafin auren. Ta koma ta sakankance, hafsa zata din ga dumbuzo abin da ta samu ta din ga kai mata, domin kuwa har ta fara tsara irin rayuwar da za ta yi, a matsayinta na surukar ƙaramin minista a Nigeria. Babu irin huɗuba da dabarun ha'inci, da ba ta koyar da hafsa ba, haka ba ta fasa shige-shige ba, cike da fatan a karon farko  hafsa ta haifo ɗa namiji, domin idan kankarofi ya mutu su samu dukiya, domin kuwa yaransa mata ne. Amma tun da hafsa ta bar gidan, wata kusan shida, ko Kanon ma ba ta tako ba, sisi ba ta turawa Zakiyya ba. Ta din ga kiranta a waya, a kan ta aiko da kuɗi, a sake bi mata malamai ayi maganin uwargidansa, kuma a kama mata shi, amma ta ce ita baya bata ko sisi. Hafsa ta sanya wa ranta, a wannan karon ba zata yi asarar kuɗinta ba, babu wani mushiriki da zai sake cin sisinta, saboda ta mallake Alhaji mu'azzam. Ta yi amfani da shawarar Jauhar, da ta bata tun tana raye, ta kama addu'a, da miƙawa Ubangiji lamarinta, tare da yi masa biyayya dai-dai iyawarta, sai kuma uwa uba gyara da take yi, yadda yakamata ba tare da ta yi abin da zai cutar da lafiyarta ko imaninta ba. Sai dai mai rai ba a rasa shi da motsi, duk da irin kula da tattalin da Alhaji mu'zzam yake yi mata, ba shi da isashshen lokacinta, kuma har zuwa yanzu ya kan bi abin da matarsa uwargidansa take so, bai fiye son ɓata mata ba, gashi kusan kowane lokaci cikin aiki yake ba shi da lokaci. A wannan karon ba ta yi yinƙurin yin fito na fito da uwargidansa ba, dan taga alamar baya son hakan, kuma ita rayuwa yar siyasa ce, a gabansa babu abin da ya yi mata zafi, da ko sako zancen matar, a bayan idonsa kuwa ba ta jurewa idan ta kira ko ta yi yinƙurin ci mata mutunci. Kuma dai-dai gwargwado kankarofi yana sakar mata kuɗi tayi yadda take so, ko kyauta zata yi a gidansu, Baba take aikawa kuɗi, ta san koba komai kowa zai amfana a kan ace Anty kawai take bawa, dan ta san ƙarshen kuɗin a yawon bin bokaye zai ƙare. Daf da azahar su Abbu suka iso gidan su Nabila, kafin nan tuni ta kammala abincin karɓar su. Abbu ne da Baba da kuma Major suka zo tare. Nabila ta yi farin cikin zuwansu sosai da sosai, sai dai Major yayi ta faɗa a kan yadda ba su faɗi abin da ya faru ba. Major kawai kallon Nabila yake yi, yadda ta fututtuke da ba ta son auren, amma tayi ƙalau da ita. Sun daɗe a gidan, sai da Major ya zaga a cikin barrack ɗin, suk sai juniors ɗin sa a aiki, duk sun yi retire. Daga nan suka je gidan Alhaji mu'azzam, suka wurin hafsa, ita ma kamar ta taka dan murna, iyaye akwai daɗi. Sai dai ba su daɗe a gidan hafsa ba, saboda yamma suka kama hanyar kano. Nabila na kitchen tana ta ƙoƙarin yin wanke-wanke, Viper ya shiga kitchen ɗin ya tarar da ita. "Sannu" Ta kalleshi ta ce "Yauwwa" "Ki na iya aikin a haka?" Ta ce "Eh mana, me ka gani?" Yayi murmushi ya ce "Bakomai, dama dai shekaranjiya suka zo, yau na so nima na yi zaman jinya, anyway sannu Abla, na so na yi appreciating iskar fankar jiya unfortunately.... Katse shi ta yi da "Ni dai na ga ta kaina da wannan fankar" Ya jingina da jikin bango, ya ce "Na yi ƙoƙari fa Abla, shekara ta nawa ina zaune haka, kodaye ba na gane komai sai 'yan kwanakin nan" "Dan Allah vi ka ƙyale ni da zancen fankar nan" Dariya ya yi ya ƙarasa kusa da ita, ya saka hannunsa a sink ɗin, yana tayata wanke kwanukan. **** Abdul shi yake kai Ramma makaranta, haka idan an tashi, idan kuma yana da ayuuka da yawa da kanta take tafiya. Mama sam ba ta son kaita makarantar nan da yake yi, tafi so ta tare, saboda gudun abin da aka iya faruwa, dan haka ta ya tan kunnen ramma, a kan lallai gara ta tare, can su ƙarata kar su ɗaukko mata magana a titi. Allah ya taimaki Abdul, hankalin Indabo ba ya jikinsa, hatta ita mahaifiyarsa ba ta cikin hayyacinta, amma shi sam hakan bai dame shi ba, yadda zai gina rayuwarsa da ta rahama yake yi. Surutun abin da ya faru da Bunkure kuwa, ya ci gaba da zaga wa lungu da saƙo, gaba ɗaya mutane suka din ga Allah wadai da yadda ta daɗe tana cutar jama'a. Viper kuwa bai bari Nabila ta yi girki ba, ordern abinci ya kuma yi musu, yana ta lallaɓata. Bayan sallar isha'i, ya kira Walid, yayi sa'a kuwa ya ɗaga. "Mai laya" "Mai zamani, ya gida ya ƙanwata?" Viper ya ce "Lafiya ƙalau, tun ɗazu nake kiranka, su Abbu sun zo fa yau, har da sirikaina" Walid ya ce "Kash, amma wallahi da na san za su zo, biyo su zan yi" "Ai gara da baka sani ɗin ba, ka zauna ka kula mini da ƙanwata, tun la'asar na kiraka ai baka ɗaga ba" "Sai magariba na ga missed call ɗin naka, muna asibiti ne, Shahida ba ta jin daɗi tun asuba muke can, sai magariba muka dawo" Viper ya ce "What? Muhsin haka muka yi da kai? Daga aura maka yarnya ka haɗata da aiki, wane irin abu ne haka?" Walid ya ce "Innalillahi me zamani meye haka wai? Fura ta sha ta ɓata mata ciki, take ta amai da gudawa muka tafi asibiti fa" "Ba wani nan, laulayi ne, matsalar aurawa tuzuru yarinya kenan, gamo da kasawa sai wannan al'amari, to ni dai idan namji ne ayi mini takwara" Kashe wayar Walid ya yi, jin abin da Viper yake yi masa. Nabila kuwa sai kallon Viper take yi, dama haka yake da tsokana har haka, kuma yana yi yana wani mazewa, kamar ba daga bakinsa suke fitowa ba. Shahida kuwa dariya take yi wa Walid, yadda ya dage yana yi wa Viper rantse-rantse. "Wallahi my kana bani dariya, ya san kunya ka ke ji, shiyasa yake yi maka wasu abubuwan, ka fiye kunya, ni har dariya ka ke bani" Yayi murmushi ya ce "Ai na fuskanci tsokanar ta wa yake yi kawai" "My ka san sai yanzu na san Yaya Al'amin yana wasa da dariya, wallahi da ko kallona ba ya yi, ban taɓa zaton yana wasa da dariya ba" Walid ya yi murmushi, yana shafa gefen fuskarta, ya ce  "Ki daina tuna bayan nan, amma Viper mussaman lokacin marigayiyya, bayan ta fara saita mu, yana wasa da dariya, kin san rayuwar ta mu ce, duk sai a hankali sai godiyar Allah. To ya ki ke jin jikin naki yanzu?" "Da sauƙi, amma ba zaka yi mini wayo ba, ni duk ka daina jin kunyar tawa yanzu" "Ai mai zamani gaskiya ya faɗa, da ya ce matsalar a ba wa tuzuru aure kenan, bai iya cin ƙwan makauniya ba" Tare suka yi dariya, cike da nishaɗi da jin daɗi. Nabila kuwa ta ɗauka, yau za ta sake, ta samu isasshen bacci, dan tun da ta fara jinyar Viper, ba ta samun bacci, ta zata ya samu abin da yake so, zai bari yau ta yi bacci. Amma sai ta riski abin da ba tayi tsammani ba, dan kusan gara jiya da yau, dan jiyan ƙyaleta kawai ya yi, yadda yake nanata zancen fankar nan, sai da ya tabattar mata da gaske tsawon lokacin da ya ɗauka, yana zaune haka ya dame shi, dan ta gazgata yadda yake ba wa fanka muhimmanci. Ɓangaren Abdallah Liti, barkwancinsa ya sanya yake da mutane sosai a kasuwa, amma hakan bai hana shi yin faɗa da muzurai wasu lokutan a kasuwar, dan ma idon Abbu yana hana shi yin wani abun. Sai dai Abbu yana jin daɗin aiki da su sosai da sosai, ba su da ƙyuya ko kaɗan, kuma ya sha jarraba amanar su, ba tare da sun sani ba, amma ko kusa ko da wasa babu wanda ya taɓa yinƙurin cin amana. Sai da ya ƙara dana sanin ɗaukar su Abba ya ɗora su a kan harkokin sa, suka din ga ɗurka masa sata, suna cutarsa. Da su Al'amin ya riƙe, da yanzu dukkanin su, sun tsaya da ƙafrsu. Sai dai ya yanke shawarar zai tallafa musu sosai da sosai, su tsaya da ƙafafuwan su, dan ya san bai isa ya biya su, wahalar da suka yi da ɗan sa ba. Samunsu a kasuwar, ya sanya wasu lokutan ko zuwa baya yi, sai ya zauna a gida ya ɗan huta, ko yaje wasu sha'anunnunkan, za su kular masa da komai babu cuta ko cutarwa. Idan yana cikinsu, sai ka ɗauka shi ne ya haife su, har shawara ya kan yi da su a kan harkar kasuwanci, bai yi da abokan sana'arsa ba, saboda su ba za su cuce shi ba ko su yi masa hassada ba. Abbun ne yake tsokanar liti ya ce "Abdallah, kai haryanzu babu wadda ku ka daidaita ne? Su sun yi aure sun bar mini kai a haka fisabilillahi, yakamata ka motsa kai ma na aurar da kai" Liti ya ce "Ai abbu wadda nake so ɗin kamar tafi ƙarfina, gani nake kamar ba za a bani ba" yayi maganar cikin damuwa. Walid sai hararsa yake yi, yadda yake sakin jiki yayi hira da Abbu shi ba ya iyawa. Abbu ya ce "Haba dai, ni da ina da wata 'yar ai da na baka, amma meyasa ka ce ta fi ƙarfinka?" Jiki a sanyaye ya ce "To ai ana ganin ni ba mutumin kirki bane ba, ba kowa zai iya jihadin da ka yi ba Abbu" "In ji waye ya ce maka ba mutumin kirki ba? Wannan wani abu ne da aka yi shi ya wuce, kuma yanzu Alhamdilillah, babu abin da za mu cewa Allah sai godiya. Kuma gaka da sana'a ka shiryu yanzu ba kamar da ba, in sha Allah za a baka, yar gidan waye idan ma baban naka ba zai tambayar maka ba, ni sai na wuce maka gaba" Liti ya ɗan yi shiru ya ce "Ƙanwar matar mai zamani ce, wata Walida a gidan su take, 'yar major ce" Abbu ya ce "Au to ashe ma 'yar gida ce, shi ne ka ke ta damuwa" "Ina jin tsoro ne, gani nake kamar ba zai bani ba, kuma Walid ma cewa ya yi na nemi wata, ba lallai a bani wannan" "Ita yarinyar kun daidaita? Kana zuwa wurinta ne?" Ya jinjina masa kai alamar eh. "An gama, ka fara tarin abin da ya sauwwaƙa ba zai gagara ba in sha Allah" washe baki liti yayi cikin matsanancin farinciki, Walid kuwa kamar ya mare shi, saboda ba ya jin kunya ko kaɗan yake wannan maganganun da Abbu. Shahida ta je har gida gaida Abbu, ta yi masa farfesun kaza, taje gaishe shi, sai da ta tuna masa da jauhar, lokacin azumi ta saka Al'amin a gaba suka zo musu sannu da shan ruwa. Rahila kuwa, ko kallon kirki ba ta yi wa Shahida ba, duk yadda shahidan ta din ga raɓarta, amma ta din ga hantararta, tana ƙarewa auren zagi. **** Viper har tausayin Nabila yake ji, domin yanzu zaman ɗari-ɗari takeda shi, saboda yadda ya addabeta, har ta fara yi masa zancen, tun da ya ji sauƙi, zata koma Kano, hutunta ya kusa ƙarewa, ya ce ba za ta koma ba, shi ma an kusa sallamar shi, zai je hutu, sai su tafi tare. Har murna take yi idan ya ɗan fita baya nan, ta samu ta ɗan sake. Da ya dawo kuwa ta shiga fargaba da tashin hankali. Da safe wurin ƙarfe tara da mintuna, Viper ya zuba wa Nabila ido da ta kasa tashi, take ta lumshe ido, alamar bacci bai isheta ba. "Abla yau ba zamu karya bane ba? Yunwa nake ji fa" Ta buɗe idonta da kyar, ta ce "Tun wurin 8 fa na tashi, na yi niyyar ɗora breakfast ɗin, kai ka hana ni, kuma ga wani irin bacci da nake ji" tayi maganar tana ci gaba da lumshe idanunta. Ya saka hannunsa, ya shafi fuskarta, ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Na sani ki na haƙuri, amma ki ƙara kin ji 'yar sugar na, duk da wasu lokutan ki na yi mini bore, but am appreciating jazakillahu bil janna" ɗan ƙara sunkuyar da kai tayi, cike da jin nauyin sa, dan haryanzu tana jin nauyinsa sosai da sosai. Sannan ta jinjinawa ƙoƙarin sa, irin yadda ta din ga shishishige masa dan ta dawo da shi hanya, da keɓewar da suka din ga yi, amma ko da wasa bai taɓa yinƙurin yi mata abin da bai dace ba, wanda hakan ne ya sanya ta ƙara sakin jiki da shi sosai. Maganar sa ce ta dawo da ita hayyacinta ya ce "Kin san wani abu kuwa?" "A'a sai ka faɗa" "Liti ne ya zo mini da wata magana, wai wata sisternki yake so, na manta sunanta, wadda muka tarar da baba uwani a wurinki a asibiti" Ta buɗe idonta ta ce "Wai Walida?" "Yes ita, wai sonta yake yi, amma ki na ganin Abba zai ba shi aurenta kuwa? Tun da kin ga ga tarihin rayuwar mu" Nabila ta ce "Me zai hana, Walida tana da sauƙin kai, kuma ba ta da dogon buri ita da Anty mamanta" Viper ya ce "Ina fatan ba zaki yi ramuwar gayya abin da yayi miki ba, ki saka a hana shi ita ba" Nabila ta ce "Haba dai, ai wannan ya wuce, ai in dai tana son shi shikenan, mu dama fatanmu kullum idan aka samu wanda ya tuba ya daina ɓarna, al'umma su karɓe shi, a mutunta shi, in sha Allah ba zai gagara ba" Viper ya ce "Mun gode sosai da sosai my sugar girl" Dariya ta yi tana tashi zaune ta ce "Wai kun gode, kamar an yi wani abu" "Bari idan muka karya, zuwa eleven, sai mu je na kai ki gidan hafsa" Cikin murna ta ce "Amma na ji daɗi sosai da sosai, na gode Vi" "Never mind, mu je ayi wanka, sai mu yi breakfast ɗin" Ta ji daɗin zuwanta gidan hafsa, ko ba komai, ta rage zaman kaɗaici. Ta din ga tsokanar hafsa wai anya ba ciki ne da ita ba, saboda yadda ta yi ƙiba. Hafsa ta ce "Wallahi ba wani ciki Nabila, jiya na gama period kwanciyar hankali ce kawai da cin abinci, ni abin ya fara damuna ma,wata shida ko ɓatan wata ban yi ba" "Kai hafsa, me aka yi da maza kwata kwata yaushe aka yi auren? Dan Allah kar ki ɗaga hankalinki" Hafsa ta rausayar da kai ta ce "To, amma ina son yara Nabila, dan Allah ki yi mini addu'a, ka da Allah ya jarrabe ni da rashin haihuwa, ina son yara sosai da sosai" Nabila ta ce "Dan Allah kar ki damu kanki, komai rabo ne kuma lokaci ne, daga yin auren ai yayi wuri ki fra wannan maganar" tayi ta kwantar mata da hankali, daga nan kuma suka ɓuge da hira, wanda galibi hirar ta karkata ga yanayin zamantakewar aure bawa junansu shawarwari, da zancen kayan likitar mata maman dr . Wadda cikin ikon Allah, magungunanta suka ɗaga darajarsu a idon mazajensu fiye da yadda suke tunani, ita mace ai yar gyara ce da kwalliya, babu borar mace sai wadda ta so. (0706 971 1327 da kayan likitar mata, bbau ruwanki da matsalar sanyi, ko fargabar amfani da kayan da baki san da yaya aka haɗa su ba, domin tsoron cutar da lafiyarku. Domin ɗaga likkafar taku kimar, ku kasance masu yawan ibada da addu'a, biyayya tare da gyara da ingantattun magunguna na gyara) Sai da suka kira Sumayya su ka yi video call da ita, domin daga abin da Nabila take missing, har da Sumayya. Cikin ikon Allah, hutun wata guda Viper ya samu, domin ya ƙarasa jinyarsa, dan haka suka nufo Kano. Nabila cike da murna ta dawo, sai dai gidan su ya sha uwar ƙura, suna zuwa mayafinta kawai ta ajiye ta hau gyara. Viper ya taimaka mata da abin da zai iya, ya tsallake ya fice, ya tafi wurin 'yan amanarsa. Tas Nabila ta ƙalƙale gidan, ta kira sumayya a waya, ta gaya mata ta dawo, ta ce mata za ta zo. Ta kuma kira Walida a waya, bayan sun gaisa take yi mata maganar liti. Da fari nuƙu-nuƙu ta fara yi, daga baya kuma ta saki jiki ta yi mata bayanin komai. A fitar da Viper ya yi, har gidan su ramma ya je, yaji daɗi da mama ta gaya masa ta koma makaranta, amma ta damu da rashin tarewarta, ta gaji da yadda sai dai ya zo ya ɗauketa su na yawo a gari. Viper ya ce kar ta damu zai yi magana da Abdul ɗin. Bayan ya koma gida yake gaya wa Nabila, da weekends Walid da liti za su zo, dan tun da aka yi bikinsu, Walid ne kawai ya zo. Ta ce masa to. Can gidansu Hafsa kuwa, 'ya'yan mama da Anty Zakiyya ta yi wa asiri, da kyar ta samu suka auru, kullum cikin ciwo suke, dan ɗaya daga cikinsu kamar zata zare, idan ta fara aljanu kamar zata haukace, hakan ya tsananta wutar ƙiyayyar da ke tsakanin su, kuma aka yi rashin sa'a, dukkaninsu babu wadda take jin daɗin zaman aurenta, ɗaya kishiyoyi sun sakota a gaba, sai da aka yi saki biyu a shakera biyu. Ɗaya kuma dangin miji da maƙwabta, sun hanata sukuni, ga miji ba ya son haihuwa. Abin duniya ya isheta, ta rasa abin da yake yi mata daɗi, ga Tijjani ya auri wata fitinanniyar yarinya da ba ta da kunya, ba ta ganin mutuncinta ko kaɗan, shi kuma ya zama tamkar soko, sai abin da take so shi yake yi, ba ya ji ba ya gani a kan matar nan, bai ƙi ya ɓata da kowa ba a kanta, ciki har da maman. Dan idan ta yi masa ƙorafi a kan matar, sai ya daina zuwa gaisheta. Saifu ne dama mai ɗan dama dama, shi ma kuma ba ya ji, ya haɗa kai da yaran masu kuɗi, yana ta rashin ji, duk da ya rage, ga kuɗi yana samu, amma ya fi mayar da hankali a kan shaye-shaye da kashewa 'yan mata kuɗi, sam ba ya yi wa rayuwarsa wani tanadi. Waɗannan tarin matsalolin ne, suka haɗu suka addabi zuciyar mama, ta kasa sukuni da jin daɗin rayuwar, duk in da ta motsa ɓacin rai da damuwa sun baibiyeta cikin yaranta kowa da halinsa. Kawai aka wayi gari tana wanka, ta yanke jiki ta faɗi a cikin banɗaki, aka ɗauketa aka kaita Asibiti, a nan aka tabattar da ta samu shanyewar ɓarin jiki. Ba ta iya yi wa kanta komai sai dai ayi mata, hatta najasa a kwance take yi, kasancewar jinya ba abu ne na ɗan lokaci ba, ya sanya yaran nata suka fara ƙosawa suke bata wahala. Hakan bai zame wa Zakiyya izina ba, dan a iya cewa ita murna ma tayi, yanzu miji ya zama nata itakaɗai. **** Liti sai ƙarewa gidan Viper kallo yake yi, an zuba wa Nabila kaya na alfarma, gidan yayi kyau sosai da sosai. Nabila ta gabatar musu da kayan ciye-ciye, take cewa Walid "Shi ne yau baka kawo mini Shahida ba" "Ai ita na kawo ta ma, ke fa baki taɓa zuwa gidanmu ba" Tayi murmushi ta ce "In sha Allah zan zo, ai ina son zuwa ziyara sosai da sosai, dan ba sai na jira Vi ba, shi sabgoginsa da yawa". Suka hau abinci da ci, Walid yana ta santin abinci, amma liti da ya karkace sai cewa ya yi "Abincin nan ya kusa kamo na 'yar madara daɗi, ita fa miyar 'yar madara sai ka kwana uku kana jin magginta a bakinka" Walid ya ce "Sannu faisal, ka tsayar da kunnuwa kamar zomo, ka na ta gizo, ka yi wa mutane shiru" Ta basar ta ce "Vi wai yaushe ɗan mama zai dawo ne?" Viper ya kalleta ya ce "Sai ya shekara biyu ai, in sha Allah zan je na gano shi" "Har shekara biyu, bai yi yawa ba?" "Ni da na yi biyar mutuwa na yi?" Tayi murmushi ta ce "To ai kai kai ne, shi kuwa abin tausayi" Yayi murmushi ya ce "Shi ma zai jure ai" Walid ya ce "Ina fatan Viper ne ya daka sakwarar nan, dan ta yi daɗi ta daku" Ta ce "Mara lafiya ne zai daka? Haryanzu hannunsa yana yi masa ciwo fa" Liti ya sake kallon falon ya ce "Ohh Allah sarki yar madara, gidanku na tuna Viper, da ta tare babu ko plasta, aka saka mata kayanta a ciki haka, gashi ta mutu, wata ce take morar arzikinka" Viper dai bai yi magana ba, Nabila ta tashi ta ce "Bari na shiga daga ciki, ku gaida gida zan ɗan kwanta" Viper ya kama hannunta, ya yi kissing bayan hannunta, ya ce "Allah ya ƙara zaƙin hannu, abinci ya yi daɗi sosai" Cikin jin kunya ta ce "Allah ya ƙara buɗi, cefane yayi kyau sosai" ta tafi tana murmushi. Liti ya ce "Haryanzu ina jin ba daɗi, idan na tuna ba jauhar ce ke more soyayyar nan ba" "Abdallah" Viper ya kira sunansa yana kallonsa. Ya kalle shi. "Ka daina yi wa Nabila abin da ka ke yi mata, son Nabila son Jauhar ne. Wani darasi da na ƙara koya a rayuwata da Jauhar, shi ne dama sau ɗaya take zuwa a rayuwa, ko ka yi amfani da ita ko ta wuce. Na samu dama na saka halaccin da Jauhar ta yi mini da soyayya da kulawa, amma ban yi ƙoƙarin hakan ba, sai a ƙarshen rayuwarmu, kuma mutuwa ta zo ta rabamu. A yanzu wata damar na samu na saka halacci da alkhairi, dan haka a daina kushe mini Abla please" "Tuba nake maigida an daina in sha Allah" Ya tashi ya yi musu rakiya, sai da ta jiyo falon shiru, sannan ta fito ta hau gyarawa. Yayi mamakin bayan dawowarsa, da take masa dan Allah su je su duba mama a asibiti, tun su na Abuja, aka ce mata tana asibiti babu lafiya. Shi mamakin da take bashi, kamar gaba ɗaya rayuwarta ba ta da riƙo, komai girman laifin da aka yi mata kuwa, da ta gama buyaginta, sai ta saukko. A daren suka je suka dubata, Nabila har da ba su kuɗi, sai da ta yi kuka, ganin yadda bakin maman ya karkace, sai zubar da yawu yake yi, ga wani irin warin kashi da take yi, duk da da pampers a jikinta, da alama tun safe ba a cire mata ita an canza wata ba. Da daddare suna kwance, tana jikin Viper, ta ce "Vi" "Mmm" "Dan Allah in tambayeka mana, amma kar ka ji haushi Please" Ya ce "Idan kin san zan ji haushin kar ki yi" "Am curious" "Go ahead" "Na ga ka na da kishi sosai, amma na ga kamar akwai shaƙuwa sosai, tsakanin Jauhar da su yaya Walid" Murmushi ya yi mai sauti, tare da shafa bayanta ya ce "Haka ne, dan ma Allah ya jiƙan rai Nura baya raye, ta fi shaƙuwa da shi sosai da sosai. A lokacin da ta shigo rayuwata, daga ni har su babu wani mai guiding ɗin rayuwarmu, ba mai saka mu, babu mai hana mu, abin da muke so shi muke yi. Bayan ta shigo rayuwata, ta fara ƙoƙarin nuna mana mu ma mutane ne. Tana da kirki da sauƙin hali sosai, a duk lokacin da na shiga matsala, babu wanda yake tsayawa a kaina, sai ita, su kuma su na dafa mata, babu wanda zai saurareta idan ba su ba. Ko sakakken abinci ta yi, sai ta ajiye musu. Gashi tana matuƙar girmamasu, saboda ta san dai babu wanda ya damu da mu, sai su ɗin dai. Saboda ita muka daina askin banza, kamar babarmu, haka za ta zauna ta yi ta mita, bayan na haɗu da Nura kuwa, tun da ta fuskanci matsalarsa shi ma ta rashin kulawar iyaye ne, da ƙarancin shekaru, take tausaya masa. Ya girmeta, amma shi ne ɗan aikenta, har kasuwa yawon sayo mata kayan shirin dutse shi yake yi mata, ina jin kishin ba bana ji ba, amma na yadda da ita, kuma idan na wulaƙanta su, saboda su daina zuwa in da take, idan na shiga matsala wa zai taimaka mata?. Ta kai ta kawo, Nura sai ya samo abin sa, bai kalli in da nake ba, sai dai ya zo wurinta. Idan matsala ce da shi ma, ita zai gaya wa saboda ni masifaffe ne, ta rayu da mu da tausayi ne, da kulawa babu ƙyama da jin cewa bamu da amfani, shiyasa Liti kullum cikin yabonta yake. Ta shiga cikin tashin hankali, ta kaɗu sosai da mutuwar Nura" Ta sauke numfashi ta ce "Na fahimta, Allah ya yi musu rahama gaba ɗaya" Ya ce "Amin my sugar girl" "Bari zan ɗan je na dawo" Ta kalleshi ta ce "Yanzu kuma? Ƙarfe tara saura fa, haba Vi" "Ba zan jima ba, ki yi haƙuri yanzun nan zan dawo fa" Ta ɗaga shi ta ce "To a dawo lafiya, banda rigima" ya sumbaci goshinta yana murmushi ya sauka. Sai dai ba ta san ina za shi ba, ba ta san lokacin da ya dawo ba, dan sai asuba da ta ji yana tashinta tayi salla. Gidansa da ya zauna da Jauhar, ya tafi, gidan ya yi ƙura sosai, saboda ya kwana biyu bai zo ba. Ya haska gidan da fitilar wayarsa, kamar walƙiya ƙwaƙwalwarsa ta tariyo masa wani moment da suka yi. Ta shigo ta tarar da shi a falo, ta ɗago masa wata jarka ta ce "Master, waye ya sha wannan abin?" "Ni ne, ba lemo ba ne ba?" cikin halinta na shagwaɓa ta ce "Master magani ne fa" "Haba dai, na basir ko shawara? Ni fa in ce, ai na zata lemo ne da, amma bakomai ai tun da maganin basir ne" Kamar ta yi kuka ta ce "Ni meye haɗina da wani basir dan Allah, kai komai na ajiye sai ka cinye, da wanda na baka da wanda ban baka ba, har nawa da naka duk sai ka haɗa ka cinye" tayi maganar tana hararsa. Yayi mata shiru, ta gama fushinta, sai da ta manta, sannan ya ce "Ai ki na da kuɗi, a kuma haɗo miki wani mana, ke ki na neman kuɗinki da kyar, su na yi miki wayo, su na karɓar miki kuɗi, suna haɗo abin da baki sani ba su na baki" Ta kalleshi ta ce "Su wa?" "Masu ce miki ki sai maganin mana, ai ina jinku, ni da na zata lemo ne ki ka yi ba ki san mini ba, shi ne zan sha rabona sai daga baya na fuskanci menene a ciki, amma bakomai ai ni na sha miki maganin, zai yi miki amfani" banza ta yi masa, ta ƙi kula shi. Dariya ya yi ya ce "Hajiya magana nake fa" "Sai dai ka yi kai kaɗai, ba zan kula ka ba" Murmushi ne ya suɓuce wa Viper, ya din ga jin tamkar ya buɗe idanunsa ya ganta. Ya jima a gidan, sannan ya fita ya nufi hanyar gida. Wurin ƙarfe takwas da rabi, Nabila ta fito tana kiransa, dan ta farka baya kan gadon. Waya ta tarar da shi yana yi. "Walid jiya kasa bacci na yi, na je gidanmu ne, na daɗe a can sai kusan ɗaya saura na koma gida. Ina ga zan sayar da gidan nan ne, ko kuma a gyara shi a zuba 'yan haya a ciki". Ƙoƙarin barin wurin ta yi, ya ɗago suka haɗa ido, ya katse wayar ya ce "Ranki ya daɗe, ya aka yi ne? Ko in zo?" Ta girgiza masa kai ta ce "Dama waya nayi da Abba ne, na fara yi masa maganar su Walida ne, amma na ga kana waya, bari na shiga ciki" ta ƙarasa maganar a gurguje, kamar mai tsoron wani abu, ko mara gaskiya. Mintuna goma, ya ji ya kasa jurewa, ya tashi ya shiga bedroom, ya tarar da Nabila ta zubo da kaya tana ninkewa. "Abla" ta ɗago ta kalleshi, ta mayar da kanta ta sunkuyar. Takawa yayi gabanta, ya karɓe rigar hannunta, ya ce "Kalle ni, menene?" Ta sunkuyar da kai ta ƙi kallonsa. "Abla am talking to you" kawai hawaye ya fara gangarowa daga cikin idanunta. "Ya Salam Abla why, kishi ki ke?" Tafukan hannayenta ta saka a kan fuskarta tana kuka mai tsuma zuciya. Cikin rikicewa ya ce "Ki fahimce ni abla, ki tsaya na yi miki bayani" yayi maganar yana riƙe hannunta. Girgiza masa kai ta yi, ta ƙwace hannunta ta fice daga ɗakin. Ya dafe kansa cikin tsananin damuwa ya sake bin bayanta. ** Indabo kamar yana kan ƙaya haka yake jin zamansa a Nigeria, gani yake komai ma zai iya faruwa. Da sassafe ya yi sallama da matarsa, bai tsaya ya saurari Abdul ba, ya tafi airport. Sai dai yana cikin jirgi, wani mutum da facemask ya bashi wata takarda ya tafi, bai san waye ba, kuma mutumin bai yi masa magana ba, bai tsaya ba domin amsa tambayar da Indabo zai yi masa ba. Ayshercool 08081012143 Bin bayan Nabila yayi yana kiran sunanta, amma ba ta tsaya ba, ya cim mata a ɗaya bedroom ɗin, tana ƙoƙarin rufe ƙofa. Ya buɗe ƙofar ya tsaya yana kallonta, fuskarta ta koma ja, haka idanunta ma sun yi jawur. Jiki a sanyaye ya ce "Abla, dan Allah ki tsaya ki saurareni, na yi miki bayani ba yadda ki ke zato ba ne" Girgiza masa kai ta yi ta ce "No need, ba sai ka yi ba, na riga na fahimta" "Ba ki fahimta ba abla, kin yi mini gurguwar fahimta, dan Allah ki tsaya ki ji" Cikin kuka ta ce "Ni ba sai na ji ba, na riga na fahimta, ba zan taɓa samun gurbi a zuciyarka ba, ni ka aureni ne kawai ka din ga kallon hoton jauhar, ba zaka taɓa so ma ba, this is the chance you ask me to give you, shikenan na fahimta" Diriricewa yayi ya ce "Ba haka bane, baki fahimce ni" "Ba sai na fahimta ba, your actions show's, da tuntuni ka bar ni na tafi a kan yadda na bar wa zuciyata, na aurenka shi ne sabuwar jarrabawar da zan fuskanta, ka yi mini maganganun da suka sanya na ji na aminta ina da kima a idonka, amma bakomai" Riƙota yayi yana goge mata hawayen fuskarta ya ce "Ko ba zaki saurare ni ba, ki daina kukan nan dan Allah ba na so" fizgewa ta yi daga jikinsa, ta shige toilet, yana jin yadda ta fashe da kuka mai tsuma zuciya. Har cikin ransa yake jiyo kukan nata, ya nemi wuri ya zauna jiki a sanyaye, tun yana sanya ran zata fito, har ya haƙura ya tashi ya fita. ****" "Na san wasiƙata zata iskeka a dai-dai lokacin da yakamata, kafin na jaka da nisa, bari na ɗan ja ka baya, zamanin da kana yaron 'yan siyasa, kun zo garinmu wani sha'ani, aka kai mu wurinku, wai zaku bamu tallafi, aka haɗamu 'yan matasan yara marasa galihu, aka kai wa uban gidanka, ya zaɓi wanda zai lalata, saɓanin cewar da aka yi za a bamu tallafin karatu da sana'a. Ina cikin waɗanda bai zaɓa ba, dan haka ban san me za ayi musu ba, na shiga damuwa burina ba zai cika ba na karatu, ba a zaɓe ni ba, ba zan samu tallafi ba. Ka yi amfani da wannan damar ka keta mini haddi, da sunan zaka saka ubangidanka ya bani tallafi. Matan da ka lalata da yawa, na san babu lallai ka tuna, sai dai shi irin wannan mikin, ba ya taɓa goguwa a zuciyar wanda aka illata. Naja'atu Bunkuren nan dai, da ka lalata da ƙuruciya a garin bunkure lokacin kana yaron ɗan majalissa, ni ɗin ce dai, ƙaddara ta sake haɗa mu, ba tare da ka gane ni ba. Sai dai ba tare da ka sani ba, ka cika alƙawarin da ka yi, na tallafar karatuna, kuma muka ɗora daga in da ka dasa aya. Ganin ina morarka, ya sanya na haɗiye mummunan ƙudurin fansar da nake da shi a kanka. Sai dai duk da haka, na yi shirin ko ta kwana ta kowace irin fuska, saboda sanin tsagwaron mugunta da zaluncinka. Lokaci ya yi da ka ke tunanin, ka ci moriyar ganga ka ya da kwauronta, ina! Idan har ka zauna a gida Nigeria, tonon sililin da zan yi maka ba zaka taɓa sha ba, haka zalika in da zaka ma ba zan bar ka ba, duk in da zaka shiga a faɗin duniya sai na kawo ƙarshenka, dan haka ya rage naka, ko ka dawo Nigeria, ko kuma ka tafi duk in da ka ke so, sai na kawo shafe tarihinka ta hanya mafi muni, zai zama daidai da ɗaukar fansar abin da ka yi mini a baya, aikin da na yi maka tsawon lokaci ma kuma ya zama halacci ga ɗawainiyar da ka yi da ni, na barka lafiya" tamkar zuciyarsa zata faso ƙirjinsa haka take bugawa, sam bai san ta ina yakamata ya fara ba, ya koma Nigeria ko kuma ya ƙarasa Saudiyya?. Nan ya shiga lissafi, me take tunanin ta ƙulla masa, da har take iƙirarin kawo ƙarshen sa a duk in da ya shiga a faɗin duniya? Har labarin lalatar da ya taɓa yi da yarinya a garinsu ya taɓa bata, amma ba ta taɓa nuna masa cewar ita ce ba, ashe duk tsawon lokacin nan wani abu ne a ranta game da shi. Ya rasa abin da yake yi masa daɗi, gaba zai yi ko kuwa baya, duk iya tunaninsa ya rasa wane irin tuggun take shirya masa. ***** Abbu kuwa ya gabatar wa da maman ramma, abin da Viper ya zo masa da shi, gam da ya aureta, ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Alhaji Ibrahim, ni a wannan shekarun nawa, me nake nema da zan sake yin aure?" Ya girgiza kai ya ce "Ba fa ki yi hamsin ba, kuma auren nan duk in da aka je aka dawo, shi ne rufin asirinki, kuma sai hankalinki ya fi kwanciya, amma ki yi tunani a kai" Bayan tafiyarsa ta din ga tunani, ƙarshe dai maganar tayi ta cin ta, take gaya wa ramma. "Amma na ji daɗi mama, babu abin da zamu cewa yaya Aminu sai Allah ya saka da alkhairi, da har ya ce ki auri mahaifinsa" "Ramma ni gani nake yi abin bai yi tsari ba, goɗai-goɗai da ni na hau yin aure?" "Mama ai mu ma sai mun fi jin daɗi ace ki na da aure, aure security ne, dan Allah ki amince kar ki ce a'a" Ta ce "Ai abin ne sai a hankali, amma zan yi addu'a dai" "To sai mu tayaki addu'ar, kin ga nan gidan ma, bamu sani ba ko Daddy zai yi amfani da abin sa, kin ga ya yi mana ƙoƙari, kalli shi yake ciyar da mu, yake yi mana komai, kin ga kuma yau da gobe sai Allah. Amma idan aure ki ka yi ai mijin ba zai gaji ba, tun da hakkinsa ne" shiru ta yi tana kallon ramma, tabbas maganganunta haka suke, ita ba ma tayi wannan tunanin ba, dan haka ta ce "Kuma fa da gaskiyar ki rahama, amma ni duk na fi son na ga kin tare tukuna a naki ɗakin" "Eh, ya ce babansa ya bar ƙasar, ya kuma gama gyara in da zamu zauna, ya canza shawara yanzu, wai zan tare amma fa har kayan ɗakin duk ya saka" Mama ta ce "Ai ni wannan mijin naki, rigimarsa ta yi yawa, na ma daina ce masa ya bari, Allah ya taimaka" ramma a zuciyarta ta amsa da Amin. Nabila kuwa fafur ta daina sauraren Viper, duk rarrashin da ya so yi mata, fafur taƙi tsayawa ta saurare shi. Zata dafa abinci ta bashi, da duk wani abu da yakamata ta yi masa, amma ba ta zama in da yake, babu hira babu duk wani abu na soyayya da take yi masa. Duk yadda yake murnar hutun da ya samu, zai zo su samu isasshen lokacin da zai bata kulawa da soyaya, amma komai ya ɓaci. Zaman gidan ma ya daina yi masa daɗi ko kaɗan, duk ɗaukinsa da son kasancewa da ita, yanzu fargabar tunkararta ma yake yi, dan sam babu fuskar hakan, sai yayi ta maza yake iya tunkararta, shi ma sai dai yayi kiɗansa da rawarsa shikaɗai. Sosai yake jin tausayinta, sai dai taƙi ba shi damar ya fahimtar da ita abin da yake son ta sani. 'yan gidan Nabila su suka zo mata wuni, har da Walida da baba magajiya, dama bata saka ran ganin Sauda ba, har da Anty. Ta ji daɗin zuwan na su, kuma babu wanda ya fuskanci tana da damuwa, suka wuni suka yi wasa da dariya, sai da ta ji kamar kar su tafi. Abu kamar wasa, Viper ya daina cin abincin Nabila, idan ma ta ajiye ba zai ci ba, ya koma kwana a ɗaya ɗakin, hakan ya saka a jere kwana biyu baya kwana a gida ba ma ta sani ba, sai kwana na uku, da bata ganshi a gidan ba, wunin ranar. Bayan magariba sai ga Walid, ta yi masa maraba ta karɓe shi hannu bibbiyu, bayan sun gaisa ya ce "Barrister, meyafaru ne tsakaninki da mai zamani, muna murna an yi aure komai kuma zai wuce, shi ma zai samu nutsuwa yanzu ya ji daɗin rayuwa kuma sai a fara rigima?" "Wani abin ya ce na yi masa?" "Bai faɗa ba, amma alamu sun nuna, kamar a gidan da muka zauna yake kwana, me yayi zafi haka?" Cikin mamaki ta kalle shi ta ce "Kwana kuma? A can yake kwana?" "Wallahi Nabila da gaske nake yi miki" Kawai ta fashe da kuka ta ce "To ni ya zan yi ne? Duk iya ƙoƙarina baya gani, Jauhar ce kawai a ransa, ni ba ni da wani gurbi a zuciyarsa. Zuciya ce fa a ƙirjina, ina son 'yar uwata, amma abin da yake yi mini yayi yawa. Muna tare da daddare har ya kwanta ya ce mini fita zai yi, sai ji na yi kuna waya, wai gidan da suka zauna ya tafi, a wannan daren ni bani da amfani kenan? Ba zan hana shi tuna Jauhar ba, amma ni fa? Kodayeke dama ni na ce ina son shi, dole na jure duk abin da zan gani" Walid ya ce "Subhanallah, kuskuren fahimta ne Nabila, tun yamma muka yi magana da shi, ya ce mini ya ji wani wa'azi, an ce gado nauyi ne a kan mamaci, har sai an raba ake sauke masa wannan nauyin. Shi ne ya ce mini tun da kema gaki, kina cikin magadanta, zai je ya duba gidan, yayi magana da su Baba, ina ga tun zuwan da ku ka yi, bai sake zuwa ba. Da safen ma, da muka yi magana ce mini yayi abin ne yake ta damunsa, ya kasa bacci, ya ji bai kyauta ba ace tsawon wannan shekarun ba a sauke wa Jauhar nauyi ba, kuma baba bai yi masa magana ba, kawai ya fita a daren, ya je ya sake dudduba gidan, ba wai dan baki da amfani ba ne ba Nabila. Wallahi kulawar da ki ka samu, Jauhar ba ta sameta daga gare shi ba shi fa yanzu duk wannan abin da yake yi, ihu ne bayan hari kawai, amma wallahi yana sonki Nabila. Kin san sunanki da nasa ya hargitsa ya fitar da sunan da yake kiranki da shi Abla? Ki din ga yi masa uzuri, a hankali zai daina, zamansa da Jauhar ba abu ne da zai manta lokaci guda ba, yarinyar ta sha wahala ne sosai, kuma ba ta wani more shi ba, an kashe ta a dalilinsa. Da bakinsa yake faɗar ki na da haƙuri matuƙa da kawaici, amma ina ƙara baki haƙuri, dan Allah ku sasanta" Tayi ajiyar zuciya, ta jinjina kai ta ce "Wallahi ina yi masa uzuri, shi ma ai ya sani amma In sha Allah zan ƙara, na gode sosai da sosai " "Yauwwa Nabila, ai wallahi tun da ya ce mini wai kin goyi bayan soyayyar liti da ƙanwarki na sara miki, ba ki da riƙo, kuma ki na da haƙuri sosai da sosai, Allah ya baku zaman lafiya ya ƙara muku fahimta juna" Ta amsa da Amin, tayi ta masa godiya, ya tafi. Kamar ta kira Viper a waya, sai ta ƙyale shi, sai da gari ya waye, tayi girki ta shirya ta fita. ***** Cikin matsanancin tsoro da fargaba, indabo ya sauka a airport, yana ta tunanin abin da ka iya faruwa, na sharrin da Bunkure ka iya ƙulla masa. Sai dai ya ga ya wuce airport lafiya, babu abin da ya faru, har ya isa masaukinsa, bai haɗu da wata matsala ba. Ya kira abokansa ya sanar musu takardar da Bunkure ta aiko masa da ita, suka bashi ƙarfin gwiwar ka da ya damu, barazana ce kawai ba wani abu ba, yayi zamansa zuwa lokacin da komai zai daidaita. Kankarofi kuwa yana ta campaign ɗin sa, na takarar sanata, kujerar da Indabo yake kai. Kuma yana ta ci gaba da samun karɓuwa ta kowace kusurwa. Jidda ƙanwar indabo kuma tana ta nacin sai ta koma ɗakinta. *** Kamar daga sama haka Viper ya ji sallamar Nabila, sai dai bai iya amsa mata ba, cikin ɗakin ta shiga, aikuwa ta same shi a zaune a kan katifa. A ranta take mamakin halinsa, daga samun saɓani yayi yaji, ƙasan zuciyarta, take addu'a Allah ya sa bai sha wani abu ba. Ba ta ce masa komai ba, ta ajiye flask ɗin, ta ƙarasa kusa da shi ta zauna, bai kulata ba, ta saka hannunta ɗaya a bayansa, ɗaya kuma ta juyo fuskarsa ya kalleta, ta marairaice ta ce "Na zo biko ne, am sorry Vi, son da nake yi maka ne ya janyo komai, kuma tunanin da nake yi, ba ni da matsayi a wurinka ne ya sanya nake shiga damuwa, but am sorry" bai yi magana ba ya ci gaba da tsareta da idanunsa. Ta shafa fuskarsa ta ce "Talk please" kamar gunki yaƙi magana. "Please talk Vi" "I love you" yayi maganar yana tsareta da ido. Idonta ne ya ciko da hawaye ta ce "And you mean it?" ya jinjina mata kai alamar eh. Rungume shi ta yi, hawayen farinciki na zubowa daga idanunta, gadon bayansa take shafawa zuwa kansa ta ce "Dama zaka iya bani gurbi a zuciyarka?" "Na daɗe da baki Abla, baki yadda da kanki bane ba, shiyasa ki ke ganin kamar ba da gaske nake ba. Tashin hankalin da na shiga, da na ji an ce gado nauyi ne, ya sanya na kasa jurewa na tafi a daren, communication gap aka samu a tsakanin mu, dole mu zama masu saurarar juna da yi wa juna uzuri domin zaman auremu ya ɗore kuma ya yi daɗi. Na yadda ke ba Jauhar ba ce ba, kuma ina ƙoƙarin na rayu da ke a Nabilanki, amma sai kin yadda da kanki, kin kuma rage zargi. Abla ina yawan gaya miki Al'amin ba butulu bane ba, bana manta halacci komai ƙanƙantarsa kuwa. Balle ke naki da ceto raina, hankalina kacokan ki ka yi, rayuwarki ki ka saka a hatsari mai ban tsoro ki ka ceto ni, tayaya zan zama butulu, a ɗakin nan na kusa ajalinki, amma bai hanaki ci gaba da bibiyata ba, wane irin butulu ne ni da zan kasa buɗa miki zuciyata ki shiga? Ki manta da matsayin Jauhar a zuciyata, ki kalli kanki ke ɗaya kawai, wasu lokutan wasa nake yi miki a wasu abubuwan, amma tun da ba kya so, in sha Allah na daina, amma ina ƙaunar 'yar sugar, wannan kalaman ko 'yar madara ban taɓa gaya wa ba, sau ɗaya na taɓa furta wa jauhar ina sonta a rayuwata, daren da za a kasheta, amma ke ba na son na maimaita wannan kuskuren ina sonki Nabilatul arfa, Ablana kuma 'yar sugana" Ita kanta ba ta san takamaimai kukan me take yi ba, ya ci gaba da rarrashinta, da duk kalaman da shi kansa bai san ya iya su ba, tare da ƙoƙarin wuce makaɗi da rawa. A hankali ta ce "Vi ba fa a gida muke ba" "Eh, ai ke ki ka ɓata mana honeymoon a gida, sai mu yi a nan" "Honeymoon a kango?" Tayi maganar tana murmushi, bai san lokacin da ya tuntsure da dariya ba, ya tashi zaune yana kallonta ya ce "Gidan gwaurontakar namu ne kango?" Tana daga kwance ta yi murmushi ta ce "Kogon da macijina ya din ga ɓuya ba" Ya gyaɗa kai ya ce "Ke ce jarumar da ki ka samawa wannan maciji 'yanci, ya ci gaba da rayuwa da cikakken 'yanci. Abla a lokacin da ake nemana ruwa a jallo, ba ki duba kamani tare da ke barazana ne a gareki ba, ba kya lissafa wannan, 'yanci kawa ki ke nema mini, na bar kogon da yake tamkar kurku a gare ni, wai duk tayaya zan manta wannan ne?" Ya ƙarasa maganar yana kwanciya a jikinta. Ta rungume shi sosai, tana sauke numfashi. A nan suka karya, hankalinsu kwance kamar su na gida, su ke gudanar da soyayyar su. Har Dutsen da ta kan je ta same shi, su ka je, ta din ga tuna masa wasu abubuwa da suka din ga faruwa, suna nishaɗi. Har yamma suna can, sannan suka tafi gida. Viper ya tambaye ta, a raba kayan jauhar a bata, ko a sayar a raba kuɗi kawai a bata. "Ba zan iya amfani da kayanta ba" Dumm ya ji a ƙirjinsa, amma ya daure ya ce "Meyasa?" "Zan daɗe ina kallon kayan ina tunata" Ya ce "Ko dai kishin ne?" "Ko kaɗan, rayuwarta da yadda ta rasu, ba zai taɓa barin ƙwaƙwalwata da zuciyata ba, ba zan iya amfani da kayan jauhar ba, rashin haɗuwa da jauhar a rayuwata wani miki ne za ba zai taɓa warkewa daga zuciyata ba. Idan ma an raba, ayi amfani da abin da na samu a sai wani abu da ladan amfani da shi zai isketa da mahaifiyarmu a makwancinsu" "Shikenan, zan yi magana da  Abba abin da ya ce shikenan" Gidan Major kuwa, Mama ta takurawa Nasir a kan ya auri 'yar ƙawarta da take so ya aura tuntuni. Aka fara shirye-shiryen biki, aka yi masa transfer a wurin aiki, zuwa kudancin Najeriya, kuma aka rage masa matsayi sosai da sosai a in da aka kai shi. Walida kuma sosai suke soyayya da liti, dan kuwa akwai shi da shiga rai. Sosai Viper yake ƙara ganin kimar Nabila, saboda rashin riƙonta, maganar bikin Sumayya ita ma ta taso, Nabila su na ta shirye-shirye. Viper sai da ya samu Liti, shi ma ya ja masa kunne, a kan abubuwan da yake yi wa Nabila. Nabila ta sake komawa duba mama, an sallamota daga asibiti tana gida, sai dai wata irin wahalalliyar jinya take yi, gaba ɗaya yaran babu mai tausayinta. Har gidan su Shahida ta je, ta zazzagaya ta sada zumunci. Bayan ta dawo, ta tarar da Viper yana ta mita. Ta ce "Meyafaru ne?" "Kuɗin da muke rabawa na ribarmu, na wurin shayin nan, wai ba za su bani ba, wurin refilling ɗin gas, Walid zai din ga zama idan ya dawo daga kasuwa, zai din ga zama". Ta ce "To menene a ciki, idea ce mai kyau" "To ai ni kuɗi nake so, harkar bikin nan na kashe kuɗi sosai, na sakankance na saka rai, suka ɓullo da wannan maganar" Ta ce "Vi ai idea ce mai kyau, zaman haka ka dogara da aikin gwamanti kawai, ba zai yiwu ba, gashi shiru an ce za ayi maka ƙarin girma amma haryanzu shiru" "Wannan ƙarin girman duk matsala ne" "A'a ina fatan mu samu ci gaba, a kan komai" Cikin ikon Allah aka saka ranar tarewar ramma, kuma maman ta amince da batun auren baban Viper. Nabila ta mayar da hankali wurin gyara ramma ma, ta biya kuɗin yi mata gyaran jiki, sannan ta saka maman yusuf likitan mata haɗata. Viper ya yi ta mita, saboda Nabila ta koma aiki, haka abubuwa suka yi wa Nabila yawa, zama matar gida babu sauƙi ga komawa aiki. A haka lokacin hutun Viper ya cika, zai koma bakin aiki. Daga shi har ita kamar su cinye juna, dan tun bayan da suka shirya, yake ta ƙoƙarin kare duk wani abu da zai sanya ta ji babu daɗi, ita ma daga nata ɓangaren tana ta ƙoƙarin kiyaye abubuwan da zai janyo su samu saɓani. Tun dare ta haɗa masa jakarsa, ta yi masa snacks, ta yi masa cincin da dambun nama, yadda zai daɗe yana amfani da shi. Sun sha soyayya ranar, kamar kar su rabu. Da safe wurin ƙarfe goma, ya tafi duk sai ta ji babu daɗi, gidan yayi mata wani iri. Kwanan Viper biyu da tafiya, Walid ya rako liti har gida, ya zo ba wa Nabila haƙuri. Nabila ta ce "Da zan riƙe abin da ka yi mini a raina, hatta alaƙarka da Vi sai na rabata, duk da tasirin shekarun da ku ka yi tare. Kawai da ka din ga iya bakinka, wani idan ka cutar da shi da harshenka, har abada duk aikin alkhairin da zaka yi masa, ba zai shafe tasirin abin da ka gaya masa ba, Allah ya shiryeka" duk da ya ji haushin kausasan maganganun da tayi amfani da su a kansa, amma ya danne. Bayan sun fito yake cewa Walid "Yanzu da gaske sai ta raba alaƙata da Viper, duk tsawon lokacin da muka ɗauka tare?" Walid ya ce "Macece fa, wallahi sai ta raba" "Kai ƙarya ne ba zai yiwu ba, ba wata mace" "Galibinmu uban meye ya koro mu daga gidan iyayenmu, idan ba tasirin kaidin mace ba, ka daina cika baki malam" Sai kuma ya ce "Kai haka ne fa, to Allah ya kyauta" Nabila ta samu labarin mutuwar Madaki, ya mutu an rasa wanda zai zo ya karɓi gawarsa, ga jikinsa babu ta in da za a saɓa shi ayi masa wankan gawa, saboda duk ya ruɓe, haka aka yafa masa ruwa aka binne shi. Da Nabila suka yi waya da Viper, ta din ga godewa Allah, da Allah ya dawo da su hanya madaidaiciya lokaci bai ƙure musu ba. Nabila ta kai wa madam Halima ma ziyara, dan sai da ta kwana biyu a wajenta, Viper ya bata damar hakan. Nabila ba zata taɓa mantawa da matar nan ba. Aka gama shiri tsaf, ramma ta tare a gidan Abdul, a lokacin tana cikin hutun makaranta. Gidan ramma ya yi kyau sosai da sosai, ana gobe zata tare ya sanar wa mummynsa, a lokacin Anty Jidda tana gidan. Ta ce "Abdul ka yi asara, 'yar matsiyata talakawa da suka tagayyara rayuwarka, yau ita ka bi kake wannan rawar kan a kanta" Abdul ya ce "Anty Jidda ban yi asara ba, gyara kuskurena na yi, kuma ke ma yakamata ki nemi yafiyar ramma, abin da ya faru da ita a gidanki, amma ki ka nuna halin ko in kula, ba zan gaji da sarawa Alhaji mu'azzam kankarofi ba, ya cika uba, kuma ni abin da yayi mini taimakona yayi" Mummy ta ce "Jidda ba fa zai gane ba, a kan yarinyar nan zai iya ci miki mutunci ma, ai ni na cire hannuna daga kan Abdul na saka masa ido, kina kallo halin da mahaifinsa ya tsinci kansa a ciki wanda har saka hannunsa bai dame shi ba, ya haɗa kai da abokan adawar ubansa ba abin da ya dame shi". Jidda ta ce "Amma kuwa Abdul ka yi asara" "Wallahi ban yi asara ba, tun da kema abokin adawar ta sa ki ka aura ai" Duk da bai ji daɗin abin da ta faɗa ba, amma yana Addu'ar Allah ya sa kar furucin mahaifiyarsa yayi tasiri a kan aurensa. Hankalinsa kwance ya kasance da ramma, cikin jin daɗi da farinciki, saboda yadda yake ji a yanzu yana da cikakkiyar dama a kan matarsa. Babban abin da ya basu mamaki, har da akwati bakwai na lefen ramma, suka tarar a gidan. Store ɗin ta na abinci shaƙe da abinci, duk wani abin buƙata da na amfani ya saka mata. Kafin ta tare ta sha nasiha, kuma sai da aka yi walima sannan ta tare. Ko sabon ango fil bai kai Abdul rawar ƙafa ba yau, a baya duk da auren ramma yake yi, ya kan ji kamar yana wani abu ba dai-dai ba, amma yanzu hankalinsa kwance, kasancewar duniya yanzu ta san ramma matarsa ce. Daren bai gushe ba, sai Abdul yana nanata wa ramma, irin matuƙar ƙaunar da yake yi mata, tare da neman afuwarta a kan abubuwan da suka faru a baya. Duk daga shi har ita ba baƙin juna bane ba, amma daren yau ɗin ya ƙara zama na musamman a cikin zukatansu, duk da a ƙarƙashin zuciyar ramma, ta na jiyo raɗaɗi da zafin rasa mutuncinta, da kuma rayuwar da ta yi, ita ba karuwa ba ita ba mai aure ba. Amma ba ta fatan sake tayar da wannan maganar, dan ta yi masa alƙawarin komai ya riga ya wuce, domin yanzu Abdul gaba ɗaya tausayi yake bata. Da safe Nabila suna Video call da Viper, ko saukkowa ba ta yi daga kan gado ba, ta kira shi ta gaishe shi. Ya zuba mata ido ya ce "Fito daga bargon sai mu gaisa" ta fito ta tashi zaune ta ce "Good morning Vi" "Morning darling, ya aiki ya gidan kuma" Cikin shagwaɓa ta ce "Am missing you" "Next week zan shigo in sha Allah, ni kaina ina kewarki like crazy, kin rame ma fa, ya aka yi ne?" "Hidimar tariyar ramma ce da na yi ta zirga-zirga, jiya dai ta tare Alhamdilillah " Viper ya ce "Masha Allah, an sha gwagwarmaya Allah ya zaunar da su lafiya ina fatan dai maman ba ta ɗaga hankalinta ba?" "Ba ta ɗaga ba, baka ga gidan rahama ba, har lefe yayi mata, ka ga rawar kai, sai dai babu kowa daga danginsa" "Tun da dai shi ya ji ya gani, aishikenan ina yi musu fatan alkhairi, yaron ma ni tausayinsa nake ji, a idonsa zaka ga yadda yake ƙaunarta. A yadda na san shi yaro ne ɗan gata mai ji da kansa. Tun da na ga ya sauke yana magiyar a bar masa rahama, na gane lallai yana son ta" Nabila ta ce "Vi ba dai son girma ba, wai yaro, mijin rammar ne yaro?" "Ban girme shi ba?" Cikin dariya ta ce "To kuma sai ka ce masa yaro?" "Eh mana, an gaya miki ni na yau ne, na kama hanyar 40yrs fa" Tayi dariya ta ce "Sannu dattijo" "Eh faɗi ki ƙara beb, Allah ya sa ki samo mana baby da wuri, kin ga na kama hanyar tsufa, in ga babyna, gashi ke ki na can ni ina nan, da mun ƙara effort kuma mu yi ta addu'a" Ta tura baki ta ce "Duk effort ɗin da saka bai isa ba sai ka saka wani? You won't kill me" Ya ƙanƙance idanunsa ya na kallonta, yana yi mata wani miskilin murmushi. "Menene kuma?" Ta tambaye shi a shagwaɓe. "Maganarki ce ta bani dariya, Abbu ma fa end of this month zai angwance in sha Allah" Waro ido Nabila ta yi ta ce "Aure zai yi?" Ya ce "Eh mana, za a ɗaura aurensu da maman ramma in sha Allah, ni na nemi ya aureta, ita ma ta fi samun nutsuwa da kwanciyar hankali" "Au kai ka bashi shawara ya yi wa maman Shahida kishiya, na ji daɗi amma ta wani fannin, baka tunanin yadda zamansu zai kasance da maman Shahida, gata ba ta da cikakken hankali?" Viper ya ce "Wacece ita da ba za ayi mata kishiya ba, haifarsa tayi?" "A'a Allah ya baka haƙuri, na ga haryanzu akwai wani abu a ranka, game da matar nan, yakamata komai ya wuce" "An gaya miki kowa irinki ne, wallahi ba zan taɓa yafewa matar nan ba har abada, ina ɗaga mata ƙafa ne kawai saboda 'yar uwata, amma ko da me take yawo ba zan yafe mata ba, ke sai anjima ma kin ɓata mini rai" "Allah ya baka haƙuri " bai jirata ba ya kashe wayar sa. Hafsa ta fara shiga damuwa, tun da ta koma gidan Alhaji mu'azzam, ko canza date na period ɗin ta ba ta taɓa samu ba, ta duƙufa da addu'a Allah ya sa tana da rabon samun haihuwa a rayuwarta, gashi kusan kullum sai Anty ta kirata tana tambayarta, ko ta samu ciki, har abin ya fara ba ta haushi. Sosai Abdul yake nuna wa ramma soyayya da kulawa, sai dai ta fara fuskantar ƙalubale daga dangin Abdul, babu wanda ya zo tariyarta, amma suka fara zuwa wai ganin 'yar ƙauyen da ta yi wa Abdul asiri. Abbu kuwa gidan da zai ajiye maman ramma daban, ba zai haɗata da Rahila ba. Sai dai tun da ya sanar mata da zai yi aure, hauka ya ƙaru tuburan, kamar ta yi masa duka saboda azabar kishi, har da iƙirarin zata cinna musu wuta a cikin gidan. Viper ya zo gida hutu, ya samu labarin abin da matar Abbu ta ce, ya ce sai ta koma gidansu an nema mata magani ta dawo, ba za ta ƙona masa uba ba, ace ba ta da hankali, idan ba haka ba ruwansa da haukanta, zai saka a fitar da ita daga gidan ta ƙarfin tsiya. Har gida Shahida ta zo tana kuka, ta na bawa Viper haƙuri, a kan yayi haƙuri, idan ta fita babu in za ta je. Viper ya ce "Shahida ba ina ƙoƙarin tozarta mahaifiyarki ba ne ba, amma da alama haryanzu karatun da duniya ta yi mata ba ta ɗauke shi ba, amma ki yi haƙuri daga ke sai mahaifina ku ka rage mini, idan ta ƙona shi ban san ya zan yi ba. Idan ba haka ba kuma a kaita asibitin masu rangwamen hankali, har sai ta warke. Shahida ta yarda da hakan, dan ita ma gani take, larurar ta mahaifiyar ta ta, ƙara gaba take yi. Abbun ma ya amince a kan a kaita asibitin ƙwaƙwalwa. Bayan kaita kuma su ka ce gado za su bata, har sai ta warke, a can zata zauna. Indabo hankalinsa ya kwanta sosai, jin ya zarta wata guda, yana zaune lafiya a ƙasa mai tsarki, ya miƙe ƙafa ya ɗora da tsula tsiyarsa. Nan gida Nigeria kuma aka ce, Indabo ya je neman lafiya ne, bashi da lafiya, amma duk wasu allowances ɗin sa suna shiga account ɗin sa. Wajen ƙarfe sha ɗaya, ya farka da kyar, kansa yana yi masa wani irin nauyi, ya duba ɗakin ya nemi yarinyar da ya kwana da ita ya rasa. Ya tashi da kyar yana dube-dube, duk ta kwashe masa abubuwa masu muhimmanci ta gudu da su. Ya duba gefen da ta kwanta, ya ga wani ƙaramin note. "Ina mai farincikin sanar da kai, samun saƙon Naja'tu Bunkure, ta ce ayi maka fatan girbar abin da ka shuka, a nan duniya da ma can in da zaka" Yana bankaɗa pillown da ta kwanta, ya tarar da ɗaurin hodar iblis, kafin ya yi wani yinƙuri, ya ji ana buga ƙofar ɗakinsa. Ayshercool 08081012143 https://chat.whatsapp.com/CHMyWTRhDYe8tdSLnXsezq Kunaneman group din dazakuringa sarin kayan kitchen afarashin sari yanda duyanda zaku karade kasuwa bazakusamu kasa d farashinmuba!!! Kuyi joining a mai nono kitchen utensils and household domin siyan dai dai ko sari dukkanin kayanmu available ne kuma farashi daidai aljihunku siyan nagari....maida kudi gida...gaskiya d amana sune takenmu!!! Ɓoye hodar ya yi, gabansa na tsananta faɗuwa ya nufi ƙofar ɗakin, yana tambayar waye?. Shiru ba a bashi amsa ba, aka ci gaba da bubbuga ƙofar. Ya buɗe ƙofar, yana buɗewa aka hankaɗo ƙofar, jami'an tsaro suka shigo cikin ɗakin, aka hau caje ɗakin. Ba ma wadda ya buɗe suka gano ba, wata jaka suka ɗaukko, ana zazzageta sai ga miyagun ƙwayoyi da hodar iblis a ciki. Rantse rantse indabo ya fara, cikin matsanancin tashin hankali, ya rasa ma me zai ce, suka saka masa ankwa, suka ingiza ƙeyarsa suka tafi da shi. **** Nabila na ta rawar ƙafar shirin bikin Sumayya, sai dai jikinta gaba ɗaya babu daɗi, wani irin nauyi jikinta yake yi mata ga kasala. Shahara da ɗaukakar da ta yi, ya sanya take samun manya manyan case, amma yanayin ɗawainiyar aure, ya sanya ta fara sarewa, gaba ɗaya jin ta take ba a dai-dai ba. Suka shirya ita da Viper ta kai shi gidan ramma, ta ji daɗi sosai da sosai da zuwansu, dan ranar Abdul ma bai fita ba, da ta gaya masa za su zo. Abincin da ramma ta yi, Nabila ta ce ba ta ci, wai ta dafa mata indomie ta cika attaruhu ta bata. Ramma ta yi murmushi, ta ce mata to, ta dafa ta bata, ta ji daɗin indomien sosai da sosai, dan a gida ba ta iya cin abinci. A hanyar komawa gida, ta saka Viper ya saya mata ƙosai, suka je gida ta dirarwa ƙosan nan, ta din ga ci da yaji tana suɗar baki. Ya dawo daga sallar isha'i, ya tarar ta kashingiɗa, tana ta lasar lemon tsami. "Abla, idan ki ka ce mini cikin ki yana ciwo, ko kuma ulcer, ko saurararki ba zan yi ba, kalli yadda ki ke azabtar da kanki da yaji, ina kallonki har da barbaɗa yaji a kam man ƙosai kina lasa, yanzu kuma kina shan lemon tsami ko?" "Vi dan Allah kar ka yi mini baki mana" "Ni dai na gaya miki ne" Aikuwa hakan ce ta faru, kwana ta yi tana yawon banɗaki, atini ya sakota a gaba, ga amai. Yana kallonta ya yi mata banza ya sha baccinsa da daddare. Da safe ma da kyar ta yi masa breakfast, almajirinta ta aika chemist ya sayo mata ruwan gishiri da suga ta haɗa tana sha. Gaɓoɓinta duk suka sage, wunin ranar ta kasa cin komai, indomien da ramma ta ba ta ce kawai take dawo mata. Cikin dare yana jin motsinta, tana ta sintirin toilet, har ya basar sai ta bashi tausayi, yadda gari yayi tsit sai kakarin amanta kamar zata amayar da kayan cikinta. Ya je ya sameta a zaune dirshen a banɗaki, duk ta fita hayyacinta. Dolensa ya fita ya bugawa maƙwabcinsa ƙofa yana da abin hawa suka tafi da Nabila Asibiti. Kwantar da ita aka yi, fatarta duk ta bushe ta zama dehydrated, leɓenta ma ya bushe sosai. Abinka da farin mutum, sai tayi busu-busu kamar korarriya. Ga tausayinta ga dariya ta bashi, iya sintirin banɗakin da ta sha ma, ya isheta punishment. "Abla ko a sayo ƙosan ne?" Murguɗa masa baki ta yi, ta lumshe idanunta, saboda har a lokacin cikinta hautsunawa yake yi. Da safe Abdul ya shigo, yana ward round kawai ya ga su Viper. Ya ce "Ya aka yi ba a kirawo ni ba? Daga tafiyarku shekranjiya har jikinta yayi haka?" Viper ya ce "Eh, likitan da muka tarar yayi mata duk abin da ya kamata ai, ba ta ji ne, ka ga gobe ba ta kuma ba, ba zata ci abinci ba, sai ta zabga yaji, abincinma sai ta gama zaɓe-zaɓe, ko ba komai ai ta hanamu bacci, in da na ji daɗi ta ji a jikinta ai, nan ɗin ne yafi mana kusa shiyasa kawai muka yo nan" Abdul ya yi murmushi ya ce "Gaskiya yakamata a tausaya mata, wataƙila baby ne ya saka take hakan, bari na yi reviewing ɗin ta" ita dai ba ta san me ake yi ba, bacci ya sake ɗaukar ta. Gwajin farko ya tabattar da Nabila na ɗauke da juna biyu, dama Viper jikinsa ya bashi, sai dai bai tabattar ba ya bar abin a zuciyarsa. Abdul ya ce "Ka ga babynka ne ya sakata cin yaji, ka ke mata dariya". Cikin farinciki Viper ya ce "Har da rigimarta, da kafirin kwaɗayinta" Ya rasa in da zai saka kansa dan murna, shi yana ta farinciki, Nabila na fama da kanta, atini ya tsaya amma jiki babu ƙwari. Sai yamma aka sallame su, Abdul ya ɗauke su a mota zai kai su gida. Duk in da aka tsaya sai ta ce Viper ya saya mata abu, duk sai dai ya kashe kuɗin jikinsa. Tun da suka koma gida kuma, Nabila ta kwanta laulayi sosai da sosai, ba ta cin komai, amai ya sakata a gaba, ga zazzaɓin dare. Jauhar ta yi laulayi ita ma, amma Nabila ta fita laulayi nesa ba kusa ba, ko fita ta daina yi, sai lokaci lokaci. Viper ne yake ta kula da ita, yana roƙon Allah ya kare masa ita da abin da yake cikinta su rabu lafiya. Ya sanya yana da rabon ganin ɗan sa a duniya. Sosai Viper yake ba ta mamaki, mutum ne mai tausayi, sai lallaɓata yake yi. Ranar wata juma'a, aka ɗaura auren Abbu da maman ramma, hakan ya yi wa Viper daɗi sosai da sosai, su Major, Baba duk sun halarta, a wurin ɗaurin auren Major ya haɗu da mahaifin liti. Classmates ɗin sa ne, tare suka yi karatu, tun lokacin secondary school, sun yi zaman mutunci, ɗakinsu ɗaya kuma kwanarsu ɗaya, tare suke komai. Rashin wayar hannu a wancan lokacin ya sanya zumuncin na su bai ɗore ba, nan hira ta wanzu tsakaninsu, hirar yaushe rabo, da hirar ƙalubale da kuma nasarorin da suka samu a rayuwa. Rahila tana ji tana gani, aka ajiyeta a gidan masu rangwamen hankali, Abbu kuma ya yi aurensa. 'yan kwanakin nan, kusan kullum idan Zakiyya ta kwanta bacci, sai ta yi mafarki da Chubaɗo, hannunta rungume da jarirai guda biyu, ɗanyen haihuwa, ƙafafuwanta duk jini, tana kallonta tana kuka. Tun da ta rasu, ba ta taɓa mafarki da ita ba sai a wannan lokacin, da fari ta maze ta basar da mafarkin, amma kuma ta ci gaba da yin sa a kai a kai, har ya zamana tana yi mata gizo a zahiri. Abu kamar wasa, ba iya ita take gani ba, wasu lokutan har da jauhar,  idan ta hange su, su na zaune su na cin abinci, da sun hangota sai su nufota. Kafin wani lokaci, ta yi wata irin rama, abin duniya ya isheta, ta kasa gaya wa kowa halin da take ciki, ba ta iya cin abinci, ga wata irin fargaba da faɗuwar gaba, sai ta din ga ganin kamar ita ma mutuwa za ta yi a kowane lokaci. Gaba ɗaya ta ji duniya tayi mata zafi, ba ta son komai, ba ta jin daɗin komai, ta tsangwami kanta kuma ta kasa gaya wa kowa halin da ake ciki, gashi tana murna yanzu miji ya zama nata, tun da mama na kwance tana jinya, amma ita ma ta kasa jin daɗin rayuwar gaba ɗaya. Kafin Viper ya auri Nabila, kallon mace mai son jiki yake yi mata, kai ba ka ce ta iya wani abu ba, saboda yadda take a sangarce, amma sai ya ga abin da ba haka ba, sam ba ta son ƙazanta, idan ya rage mata aikin gida ya fita, idan ya dawo a hakan zai tarar ta lallaɓa jikinta, ta gyara ko ina, har ma ta yi girki. Kayansa za ta saka a inji ta wanke ta shanya, su bushe ta bayar a goge masa. Sosai yake jin tausayinta, gashi lokacin komawarsa bakin aiki yayi. Cikin kulawa ya ce "Abla ko dai tare zamu tafi ne, ko na tafi hankalina ba zai kwanta ba saboda yanayin jikin nan naki" "Komawa zaka yi, babu wani abu da zai faru in sha Allah" "Yanzu ko a gidanku, babu wani wanda za a baki, ya zo ya tayaki zama?" Tayi murmushi ta ce "Maraicin kenan Vi, ba sai na gayyaci kowa ba, na san ba bani za su yi ba, Sumayya ce dai ta ce mini za ta zo idan ka tafi, kar ka damu zan iya zamana" Cikin kulawa ta ce "Abla ba kya cin abinci ai, duk kin yi wani iri" yayi maganar yana shafa wuyanta. Langaɓe masa ta sake yi, daurewa kawai take yi ne, dan kar ya ƙara shiga damuwa, dan kuwa har kuka take ɓuya tayi, ganin yadda ba ta iya cin abinci, kullum cikin amai take. Shi kansa Viper sai da ya tambayi Abdul, ko akwai maganin da za a bata ta daina aman nan, ya ce masa sai dai ayi haƙuri, lokaci ne zata daina. Lokaci lokaci, ramma sai ta yi girki, ta ba wa Abdul ya biya ya kai wa Nabila. Har Viper ya tafi, hankalinsa yana kan Nabila da ya bari, Sumayya ta kan zo ta ɗan tayata zama ta kwanar mata biyu, ita kanta tana jin tausayin Nabila dan wani irin wahalallen laulayi take yi. Sai dai duk da halin da take ciki, kasancewar 'yar dagiya ce, bai hanata kasawa tare da tsarewa ba, a duk lokacin da za a gabatar da shari'ar Naja'atu Bunkure ba. Dan ranar farko da Bunkure ta ga Nabila, sai da haɗuwarsu ta farko ta dawo mata, bayan gama saurara Shari'a sai da Nabilan ta bita, ta ce "Allon kwaikwayona, ina fatan a yanzu kin tabattar da Allah ne mai yi, babu ruwansa lokacin da ya so, zai iya ɗaukko na can ƙasan da ba a iya hango shi, ya ɗaukaka shi sai kowa ya ji shi, hakazalika ya ɗaukko na can saman ya kai shi ƙasa, sai kowa ya manta da shi. Ba zan ci gaba da bibiyar shari'arki dan fatan na ga bayanki ba, sam, na gama nawa tun da na kai ki ƙasa, na bayyana wa duniya wacece ke, zan bibiya ne saboda hakkin mutane da kuma jinin 'yar uwata da ki ka ce ya tafi a banza" Bunkure ba ta iya mayar da martani ba, aka zunkuɗata cikin motar masu laifi, aka tafi da ita. ***** Duk ƙumbiya-ƙumbiyar da ake yi, da ƙoƙarin rufe abin da ya faru, sai da abun ɓoye ya bayyana na kama Indabo da miyagun ƙwayoyi a ƙasa mai tsarki. Ramma tana zaune a falo, tana assignment, Abdul ya shigo babu ko sallama, ya wuce ɗaki. Ta bi bayansa tana faɗin "Yau kuma waye ya taɓo mini bokan turai" idanunsa ne suka tabbatar mata akwai damuwa gagaruma. "Doctor meyafaru kuma? Wani abin ne ya faru?" Ya haɗiye wani abu mai ɗaci, ya dubeta ya ce "Daddy aka kama a Saudiyya" Ramma ta ce "Subhanallah, me ya yi aka kama shi?" "Da miyagun ƙwayoyi aka kama shi, abin takaici wai a ƙasa mai tsarki" Ramma ta ce "Subhanallah, abin bai yi daɗi ba. Addu'a ce yanzu ya kamata ayi, Ubangiji Allah ya fitar da shi" Ya kalli ramma idonsa fal hawaye ya ce "Allah ya fitar da shi how? Saudiyya ba fa Nigeria ba ce ba, duk laifukan da yake aikatawa ba su isa ba, sai ya tsallaka ƙasa mai tsarki?. Har tsoro nake ji, ko idan ya koma ga Allah idan na roƙa masa rahama Allah zai karɓa? Tarin mutanen da zalunta saboda kujerar nam, a ina zai gansu ya nemi afuwarsu? Ni iyayena ne jarrabawata, da ina da iko, da ban zo a tsatsonsa ba" Cikin kulawa ramma ta fara rarrashin da bai kai zuciyarta ba ta ce "Doctor, ba a yanke tsammani da rahamar Allah, kuma shi mai rahama ne, dole a roƙa masa rahama tun da musulmi ne" "Amma kin san Allah baya yafe hakkin wani a kan wani ko? Yau ko tuba yayi ya daina laifukan da yake yi, waɗanda ya zalunta fa wasu ba sa duniyar nan, sun bar ta, a wurin wa zai nemi yafiyar? Mutanen da ya dasawa damuwa da baƙin ciki su na da yawa fa. Allah mai rahama ne da jin ƙai, amma sai da ya haramta shi a kan kansa, sannan ya sanya shi abin haramtawa a tsakaninmu, ke ki ka biya mini wannan hadisin, ni babu wani abu da za a gaya mini yanzu na ji sanyi, ina tausaya masa haɗuwarsa da Allah" Jiki a sanyaye ramma ta ce "Ka yi gaskiya, amma yanzu ai ba mutuwar yayi ba" Ya kalleta fuskarsa duk hawaye ya ce "Kin san hukuncin ace an kama mutum da irin abin da aka kama shi da shi a ƙasa mai tsarki? Muddin suka tabattar hukuncin kisa ne" gaba ɗaya sai ta rasa me ma za ta ce. Har ga Allah Abdul ya bata tausayi, amma ita ba ta ji ta damu ba ko kaɗan, albarkacin Abdul ɗin ne ma bai sanya ta ce Allah ya ƙara a zuciyarta ba. **** Hafsa ta biyo Alhaji mu'azzam, domin kawo ziyara gida, sai dai ta tsorata da yadda ta ga jikin mama ya ƙara tsananta, ta zama wata irin miskiniya abin tsoro. Sai dai ta tsorata da ganin ita ma tata mahaifiyar ta yi wata irin muguwar rama, gashi duk kauɗinta yanzu ba ta son yin magana. Ga zaman ɗaki, cikin mamaki take tambayarta ko lafiya? Ta fashe da kuka take gaya wa Hafsa abin da yake faruwa. Tayi shiru sannan ta ce "Ikon Allah, kin ga kaɗan daga illar biye-biye anty, yanzu an ce Anty Rahila tana gidan masu rangwamen hankali, ni na fara yin ciwon hauka a sanadin shaye-shaye, ke ma kuma ga alamu" Ta waro ido ta ce "Hauka kuma?" "Eh matsalar ƙwaƙwalwa, wannan alamomi ne na depression" "Wallahi na yarda da maganarki, wasu lokutan ji nake kamar na fita da gudu ina ihu, duniyar tayi mini zafi, amma ni sai nake tunanin ko matar nan ce duk da tana kwance, ta haɗa kai da yaranta suke banko mini asiri" Hafsa ta katseta ta ce "Mama babu wanda yake banko miki wani asiri, ganin Jauhar da mahaifiyarta da ki ke yawan yi, yana alamta miki, kin tafka mummunan laifi a rayuwarki, da babu lallai sun yafe miki, gashi ba sa duniyar. Shawara ɗaya zan baki, ki din ga yi musu addu'a, sannan ki dage da istigfari kuma ki daure, ki nemi afuwar Baba, sannan ki nemi afuwar ɗan uwanta babansu Nabila, da ita kanta Nabilan, tun da duk su na da alaƙa da su, idan ki na so ki samu nutsuwa. Sai kuma mu dangana da asibiti ki fara ganin likita" "Tabɗijan, kawai kuma sai na je ina cewa wani su yafe mini, da na yi musu me? Wallahi ba zani ba" Cikin takaici da mamaki, take bin Antyn da kallo, ta ce "Ba zaki ba Anty, sai abin da ya samu babar su Shahida ya same ki tukuna?" "Ya daɗe bai same nin ba, ba zani ba, ni na san asiri kawai ake yi mini, kuma ni dai-dai nake da kowane mara mutunci" Duk yadda hafsa ta so ganar da ita, ta rufe idonta taƙi ganewa. "To mu je asibiti, tun da nima kin ga da haka na warke, da aka din ga kai ni Asibiti" "Ba zani ba shi ma, ni na san maganin matsalata" haka Hafsa ta ƙyaleta, dan babu yadda ta iya da ita". Washegarin zuwanta ta tafi gidan Nabila, tayi sa'a Sumayya ma tana can, haɗuwar ta su ta yi musu daɗi, sai dai a kallon farko ta ga Nabila ta rame sosai, ba ta yi magana ba, Nabila nata nuƙu-nuƙu da hijjabi, amma sai da Hafsa ta gano ta. "Abla, wai me ki ke ɓoyewa ne? Duk ɓoyonki ana gani ai" Kunya ta kama Nabila ta ce "Ake gane me?" "Ɗan baban mana" Sumayya ta kwashe da dariya ta ce "Ai na gaya mata ana gani, taƙi yadda, mai cewa sai ta yi good 2yrs a gidan miji, kafin ta ɗau ciki, amma farawa da bisimillah" Hafsa ta kwashe da dariya ta ce "Ai kura ta san gidan mai babban sanda, ai ita ta san in da za ta iya cewa, sai ta shekara biyun ba ta haihu ba, ba dai a gidan Viper ba" Nabila ta ce "Baku da aikin yi ne, ulcer ce ta kumbura mini ciki" "Viper dai yayi ajiya, shi ya kumbura miki cikin" Hafsa tayi maganar tana dariya. "Ku da Allah, kuna munafuncin mijina a gabana, wanda idan yana nan, ko tarin kirki ba zaku iya ba, a ƙyale mini shi kar a saka ya ƙware, yana can yana aiki, kuna nan ku na gulmarsa" Hafsa ta ce "Ke abin alkhairi ne ai, Ubangiji Allah ya inganta miki ƙanwata, ya rabaku lafiya" "Amin Anty hafsyna" Sumayya ta ce "Shahida ma na ga kamar an gamu" Hafsa ta ce "Nima ma gani, ai na je gidanta" Nabila tayi dariya ta ce "Mijinta ce mini yayi baya son saka ido mura take yi" suka yi ta hirarsu gwanin sha'awa, hafsa ta ce "Dan Allah ku tayani da addu'a, nima Ubangiji Allah ya sa ina da rabon ganin jinina a duniya, ni haryanzu shiru" suka yi ta kwantar mata da hankali da yi mata fatan alkhairi. Aka koma maganar bikin Sumayya, Hafsa na ta ƙara nanata mata, kar ta kuskura ta je ta sha wani abu da ba ta san menene ba, alhalin ga likitar mata. Nabila ta ce "In dai ki na son daga shiga kema ki ɗaukko magana, ki riƙe wa kayan likitar mata wuta, zaki gane baki da wayo, laulayi is not your mate " Hafsa ta ce "Rabu da ita, ta ji da assignment ɗin da Viper ya bata" Nabila na daga kwance a kan cinyar Sumayya ta ce "Wuta balbal idan aka ƙira sunan mijina" "An faɗa Aminu Viper, mai zamani" "Ku da Allah" Nabila ta dage ta din ga lallaɓa hafsa, sai da ta kira Alhaji mu'azzam, suka kwana a gidan. Ita dai kaf 'ya'yan babansu, da aka nuna mata, babu wanda take jin tana so, kamar hafsa, ita dai tana ƙaunarta sosai. Sai kuma suka koma hirar ƙalubalen rayuwar gidan auren, tare da ba wa junansu shawarwarin da za su fishshe su. Kwana biyun da suka yi mata ta ji daɗi sosai, bayan tafiyarsu zaman kaɗaicin ya ci gaba da damunta. Babu tsammani taga Viper ya dawo, aikuwa ta ji daɗin hakan. "Vi ya na ganka ka dawo yau?" "Shi ne lokacin da aka ce ki fara zuwa awo, ina lissafe ni ai" Tun daga Abuja ya taho mata da amala, saboda ya san tana sonta, aikuwa ta ji daɗin amalar nan. Ta ci kaɗan ta ga tayi awa biyu ba ta yi amanta ba, aikuwa ta rufar mata, ta cinye tas. Kwana tayi amai, ba ta yi baccin kirki ba. Da safe ya buga wa Abdul waya, ya ce masa zai kawo Nabila asibiti, ya ce masa to. Abdul ya yi mamki, ganin cikin Nabila wata huɗu, amma ya ɗago sosai. Suka gaggaisa, ya yi mata sannu. Viper ya ce "Ya ƙanwata?" "Tana gida sun yi hutu, ga saƙo ma ta bani, wai na kawowa yayarta" yayi maganar yana nuna musu fulas ɗin abinci. "Ko menene a ciki, in dai yaji yayi yawa ba zaki ci ba, bar rawar jiki" yayi maganar yana harar Nabila. Tashi Nabila ta yi, ta buɗe flask ɗin, ƙamshin miyar jajjage ya daki hancint, tayi maza ta rufe dan da alama miyar mai yaji ce. Abdul ya ce "Ina ce mata zaku zo, ta zaunar da ni sai na taho miki da abinci" Viper ya ce "Duk in da muka je, har rawar jiki take ace mata ga abinci, kamar ba na ba ta abinci a gida" "Bana ƙoshi ne" tayi maganar tana dariya. Abdul ya ce "Maybe na gidanta ba ta iya ci, idan suna irin wannan halin sai haƙuri ai" Viper ya ce "Haka ne, amma ya na ganka wani iri, ko baka da lafiya ne?" Bai ɓoyewa Viper ba, ya gaya masa komai, Viper ya ce "Irin haka sai haƙuri, kuma ka ci gaba da addu'a, kuma kai ka kiyaye aikata makamantan laifukan da ya aikata" Kalaman Viper dai babu tausayawa ga Indabo, amma rarrashi ne ga Abdul. Ɗakin scanic suka tafi, bayan an yi wa Nabila gwaje-gwajen masu ciki. Viper yana tsaye a kan Nabila, yana riƙe da hannunta. Abdul yake gaya wa Viper, doctor Muktar ya tafi ƙaro karatu malesia. Abdul yana cikin maganar ya yi murmushi, ya kalli Viper ya ce "Congratulations bani goron Albishir" "Albishir ɗin me? Bayan dama can na san da akwai cikin?" Abdul ya ce "Ba zan faɗa ba ne, sai ka bani tukuici" Viper ya ce "Faɗi sai a baka" "Naƙi wayon, kawo kawai" Viper ya yi murmushi ya zaro dubu ɗaya ya ajiye masa ya ce "Faɗi idan yayi mini sai na ƙara maka" Abdul ya ce "Ai kai ne mayar da tukuicin, ai albishir ɗin namu ne gaba ɗaya. Twins ce dama ita ai ko?" Viper ya jinjina masa kai. "So congratulations, babynta biyu ne a cikinta, twins ne yaran" Waro ido Viper ya yi yana kallon screen ɗin injin scanic ɗin, tamkar zai gane menene a jiki. Jikinsa ya hau wata irin tsuma ya ce "Dan Allah da gaske ka ke ko da wasa?" "Yaya zan yi maka wasa da abu mai muhimmanci har haka? Wallahi da gaske nake, twins ne, kuma duk su na cikin ƙoshin lafiya" Viper ya miƙe ya yi sujudar godiya ga Allah, ya miƙe ya rasa me ma zai yi ko ya ce. Ya kwance agogon hannunsa, ya ajiyewa Abdul, ya zaro ɗaya daga zobensa na azurfa shi ma ya ajiye masa. Ya fara laluba aljihunsa, Abdul ya ce "Haba Viper, yanzu mun zama ɗaya sirikina ne fa kai, ina tayaka murna, Allah ya inganta ya raba lafiya, amma ku yi shiru kar wanda aka gaya wa biyu ne. Ga agogonka da zobenka ba zan karɓa ba" Viper ya yi ajiyar zuciya ya ce "Kar mu yi haka da kai, yarana biyu na rasa, ɗaya aka yi ɓarinsa, ɗaya kuma bai ma zo duniyar ba, yanzu Allah ya haɗa mini biyu. Na ma rasa wane irin farinciki zan yi ne, ba kai ka bani ba, saƙon kawai ka gaya mini, amma ba ka ji zuciyata ba, Alhamdilillah ala kulli halin. Na rasa jauhar, ga Nabila, na rasa yarana ya bani biyu Allah Alhamdilillah. Yayi maganar yana goge ƙwalla. Jikin Abdul ya yi sanyi, da ya tuna babansa ne silar ajalin matar Viper. Ya tuna lokacin da yake yi wa Viper kallon ɗan jagaliya, ɗan maula ƙasƙantaccen mutum da yake zuwa maula wurin mahaifinsa, yau gashi Allah ya canza komai, ya nutsu ya zama mai bayar da gudummawa ga al'umma. Ya ƙarasa ya ɗago Nabila, yana mata sannu. "Abincina" tayi maganar kamar ƙaramar yarinya tana kallonsa. "Ai dole ma a ɗaukko abincin nan Abla" "Kuma ka gaya musu su daina damuna, ko in ƙi haifarsu" Cikin murmushinsa da yake ƙara masa kyau ya ce "Za su daina in sha Allah" Abdul ya ci gaba da yi musu fatan alkhairi, da taya su murna. Tun da suka koma gida, duk in da Nabila ta yi sai ya bi ta da kallo, yana tunanin yara biyu ne a cikinta. Addu'a ya din ga yi, Allah ya sa yana rabon da ganin yaran, tare da yi musu fatan shiriya tun kafin su zo duniya, da fatan Allah ya sa kar laifukan da ya aikata su shafi yaransa. Nabila tunani ta din ga yi, na abin da za ta yi, da zai wayar wa da al'umma kai, a kan muhimmancin neman 'yancinsu, da ƙirƙiro abubuwan da za su taimaka wurin ƴaƙi da harkar daba da shaye-shaye da kuma bangar siyasa. Yanayin shirin bikin Sumayya da suke yi, ya hanata zama su tattauna yadda yakamata, ta na son ta yi magana da Viper ma, domin za ta so goyon bayansa ɗari bisa ɗari a kan abin da take ƙudurin yi ɗin. Aka yi taron bikin sumayya lafiya, aka gama lafiya, ita ma mijinta mutum ne mai rufin asiri, ya na da mace ɗaya da yara uku, cousin ɗin Alhaji mu'azzam ne, shi ne ya haɗa shi da ita ma. Major yana ta mitar Nabila kwana biyu ba ta zuwa gaishe shi, ya kirata ya ce mata shi zai zo ya ganta, amma ta ce masa ba ta nan, sai dare zata dawo. Bayan sallar isha'i kuwa sai gashi shi da Anty, tun da suka zo ta manne a wuri ɗaya ta ƙi tashi. Viper ya yi wa Major zancen rabon gadon Jauhar, za a sayar da kayanta, Nabila ta ce ba ta son kaya. Abba ya ce "Ni idan an yi wa kayan kuɗi a bani na saya, sai mu bayar sadaka Allah ya kai mata ladan". Viper ya ce "Ita ma ta ce kuɗin, ayi wani abu da su, Allah ya kai ladan kabarin Jauhar" Major ya ce "Hakan ma yayi kyau, amma a ajiye wani abu da za a din ga tunawa da ita dai" "Eh in sha Allah, ko ma muje gidan tare, sai na yi wa Baba magana muje a duba" Major ya ce "Duk yadda ka yi yayi, Allah ya saka maka da alkhairi kai ma, Allah kuma ya ƙara bamu haƙurin rashin Jauhar da mahaifiyarta" Har suka gama abin da za su yi, Nabila taƙi yi musu rakiya, sai Viper ne ya raka su, suna tafe a hanya Major yake mitar Nabila duk ta zama so silent, ko dai akwai wani ne da take ɓoyewa. Anty ta ce "Ciki ne fa da ita, take ta wannan nuƙu-nuƙun" "Kaii ciki, tun yanzu?" Anty ta ce "Ahh ikon Allah, wata nawa da yin auren?" "Lallai Major, wato Arfa ce 'ya, mu a shekara nawa muka haihu?" Ya ce "Ai ku tun zamanin baya ne, ita kuwa kamar yayi wuri, haryanzu ƙanƙantarta nake gani" "Shekara ashirin da shida?" "Eh mana, rainon ciki akwai wahala, kin ga ita ga ba uwa, ku ba tayi sakewar da za ta tunkaroku da wannan maganar ba, balle ma idan wani abin ne ku taimaka mata ba, bari na koma gida, zan kirata a waya, ko da wani abu da take buƙata" Waro ido ta yi ta ce "Sai ka tambayeta a kan cikin?" "To shi ne me? Ni uwar ni ne uban, ai cikin halak ne, mijinta ba mazauni ba ne ba, cikin fari ba ta san kan komai ba" "Amma ai ka bari mu mu tambayeta ko" "Tsakaninki da Allah yaushe rabonki da ita, ban da yau da na ce ki zo ki rako ni wurinta? Ni ba abin kunya ne a wurina ba, idan ta kama na dawo da ita gida, gani gata magajiya ta din ga kula mini da ita, ba ruwanku" Anty ta ja bakinta ta tsuke, dan ba ta ga tsari a hakan ba. Aikuwa kamar yadda ya faɗa, hakan aka yi, bayan ya koma gida ya kira Nabila yake tambayarta. Kasa ba shi amsa tayi, ta ji tamkar ta nutse a wurin, saboda kunya. "Idan kin san akwai matsala, ni sai na yi wa mijin naki magana, idan baya gari ki taho gida, ko na turo miki magajiya, ta din ga kula da ke" "Abba yana kula da ni, baba Magajiya kuma yakamata ace zuwa yanzu ta huta ita ma, ina iya yin komai ma" "Kin tabatta?" "Eh Abba" "Arfa ba na son kawaicin nan naki, Ni babu kunya a tsakanina da ke, baki da uwa a raye, kar ki bari wani abu ya shige miki duhu, idan ba zaki iya kirana a waya ba, ki yi mini message kin ji ko?" "To Abba" "Allah ne mai komai, amma ba zan so ki sha wahalar da mahaifiyarki ta sha ba" "In sha Allah" Ya ce "Yauwwa, sai da safe, ki gaida mijin naki, Allah ya yi muku albarka gaba ɗaya" "Amin mun gode, ayi wa Anty ya ta je gida" ta kashe wayar, Viper ya na kusa da ita, ya na saurarenta. "Abla" ta waiwayo ta ce "Na'am" "Kowane dangi, idan aka samu irin Abba ko guda ɗaya ne, mai jajircewa a kan zumunci, ba tare da kallon ɗora wa kansa ɗawainiya ne ba, da an rage wani abin. Mutum ne mai zafi, amma jajirtacce ya san abin da yake yi. Ke kaɗai sadaƙatul jariya ce a gare shi ko bayan ransa. Banda ladan zumunci hatta taimakon da ki ke yi wa al'umma yana da lada. Kin tsayawa dattijon nan babu ko sisi, kin tsaya wa rahama, kin tsaya mini duk babu ko sisi, kin siffantu da wasu daga cikin kyawawan ɗabi'unsa, da shi da Alhaji mu'zzam, da Walid da liti, mutane ne da al'umma ke buƙatar irin su." Nabila ta ɓata fuska ta ce "Ban da liti dai" "Haba masoyiyya, ya fa baki haƙuri. Wallahi Abdallah mutumin kirki ne fiye da yadda ki ke zato, kawai dai mutum ne da babu ruwansa da kara, zai yi abin da yake so ne, ko yayi maka daɗi ko ya kashe ka, bai damu ba" "Ai na ga alama, ni fa ban taɓa zaton ya na barkwanci ba, ranar da na fara ganinsa, a tal'udu wurin da yake sayar da katin waya, amma kayan maye yake sayarwa, sai da na tsorata. Babu alamar ɗigon imani a tattare da shi, sai fa da ya ce sai ya kashe ni, idan na sake zuwa" "Wallahi ba haka yake ba, sharrin ƙwaya ne kawai da kayan maye, Allah dai ya ƙara shirya mu, rayuwa duk ta fi yi mana daɗi a yanzu. Mutane kowa yana sonmu, yana son haɗa alaƙa da mu, har ana ɗora mana wasu nauye-nauye. Duk a baya, mu kanmu bamu jin cewa, a duniyar da mutane suke muke, hango duniyarmu muke yi daban, saboda kowa kallon mutane marasa amfani yake yi mana. Marigayiyya ce ta fara ƙoƙarin ankarar da mu, muhimmancinmu a cikin al'umma." Nabila ta jinjina kai ta ce"Jauhar ta yi namijin ƙoƙari ƙwarai da gaske, kuma in sha Allah, yana daga cikin abin da na ƙudurce a zuciyata, ci gaba da yaƙi da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, ta hanyar nuna wa wanda suka tsinci kansu a harkar, su ma 'ya'ya ne, kuma akwai amfanin da za su yi wa al'umma. Ina son da ni da kai, sa sumayya, barrister Habib, da wanda suka kamata, mu ga abin yi, idan ta kama ko ƙungiya ce mu kafa, ko mutane goma ne suka shiryu a sanadinmu, mun yi nasara" "Duk a bar wannan maganar, sai Allah ya saka kin sauka lafiya, sai ayi ta, tunani mai kyau sosai da sosai. Sumayyan nan taki ma 'yar aljanna ce da yardar Allah, na ga tana yinki saboda Allah" "Ko ba Sumayya ba, ba ka ga Abba ne yayi waliccin aurenta ba ma, ƙawar amana kenan, ina alfahari da ita" Haka Viper suka ci gaba da tattaunawa da shi da abar ƙaunarsa. Kwanci tashi asarar mai rai, cikin Nabila ya yi watanni shida, amma kamar zata haihu a lokacin, saboda girma, hakan ya saka ta daina fita gaba ɗaya, saboda nauyin cikin. Shahida kuwa matar Walid, ta fita nauyi, dan ita nata ya kusa shiga watan haihuwa. Ramma na gida ta dawo daga makaranta, tana ta sauri ta gama abin da take yi, ta san Abdul ko ya dawo, ko ya aiko a ɗaukar masa abinci. Kiran waya ta gani, da baƙuwar lamba, ta ɗaga tare da yin sallama. "Matar doctor Abdul ce?" "Eh nice" "Ok, dan Allah maza ki taho Asibiti, Doctor ne ya yanke jiki ya faɗi" "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" ta furta jikinta yayi wani irin sanyi. Ayshercool 08081012143 Jikin ramma tsuma ya din ga yi cikin matsanancin tashin hankali da damuwa, fargabarta Allah ya sa ba wani mummunan abin ne ya faru da shi ba, dan kuwa yanzu a duniya tana matuƙar buƙatar Abdul a cikin rayuwarta. Ko rasa shi tayi, ta san abu ne mai wahala samun mijin da zai tsaya a kan lamuranta kamarsa. Hijjabi kawai ta zura ta fice daga gidan ta tafi asibitin da ya ce mata zai je ganin marasa lafiya. Har an bashi ɗaki, yana kwance ana ƙara masa ruwa. Cikin tashin hankali da damuwa, take tambayar meyasame shi. Wani likita yake yi mata bayani "Bamu sani ba, ya gama ganin marasa lafiya, aka kira shi a waya, ba mu san me aka ce masa bai fi mintuna sha biyar ba ya faɗi, amma ya farfaɗo ɗazu har yake ta kiran sunanta, aka yi masa allurar bacci. Ta ɗauki wayarsa, ta saka thumb print ɗin ta, ta buɗe wayar. Call log ɗin sa ta duba, ta ga wanda suka yi waya ta ƙarshe da shi Honorable speaker ta gani. Ta kalle shi, ta san ba zai wuce a kan maganar mahaifinsa ba ne ba. Tausayin sa ya kamata, ta matsa kusa da shi tana shafa kansa, yanzu da ya nutsun nan, har wani kyau ya yi na musamman. Rashin ji da gagara ba su da wani amfani. Aka kira sallar la'asar, ta shiga banɗaki ta yi alwala, tana fitowa taga Mummy da Anty Jidda a ɗakin. Mummy ta ce "Ga shaiɗaniyar yarinyar nan" Jidda ta kalli ramma, yarinyar da take mata aiki,  wahalalliyar 'yar ƙauye tayi ƙiba, fatar nan tayi kyau. "Ramma, ke nake gani haka?" Ramma ta dake ta ce "Eh, nice anty Jidda, kin yi zaton tozarcin da ki ka yi mini Allah zai wulaƙanta ni ne? Ai shi Allah yana kishin bawansa" "Ramma ni ki ke gaya wa haka?" "Ai ba tun yau ba, na daɗe ina fatan Allah ya haɗa ni da ke, na gaya miki abin da yake raina. Duk bauta da wahalar da nake yi miki da yaranki, iftila'i ya same ni a gidanki, ki nuna baki sanni ba, in haɗu da ke ma, ki ka toshe kowacce irin kafa, ki ka wulaƙanta ni, aka hana mu shiga gidan ma, babu wata magana mai daɗi ko rarrashi, saboda ni baitil mali ce mara galihu. To da yake shi Allah ba yadda ba ya juya lamuransa ai yanzu ku na gani, ko iftila'in zawarci ma ya ishe ki" Buɗe baki suka yi su na kallon ramma. Ko a jikinta ta sake cewa "Wallahi darajar mijina ki ka ci anty Jidda, amma niyya na yi na roƙi Allah ya sa yi wa 'yar ki abin da aka yi mini, a kan idonki ki ji abin da ni da uwata muka ji, sai dai kash ƙaddara ta riga fata, yaranki ba su suka yi mini laifin ba, kuma wanda ya yi laifin ya yi tuba na haƙiƙa, kuma na yafe masa har gaban abada, amma ba dan haka ba ba zan gushe ba ina yi miki fatan Allah ya jarrabeki ke ma, ko alhakin mai gadinki da aka kashe, ya isheku nauyi". Mummy ce ta fara zage-zage, ramma kuwa ta tayar da salla, tare da jin sassauci a zuciyarta ko ba komai yau ta amayar da wani abu da yake ci mata zuciya. Wani likita ne ya zo yayi musu magana, a kan ko su yi shiru ko su fita, Abdul yana buƙatar hutu. Anty Jidda dai azabar mamaki ya hanata magana, kallon ramma kawai take yi, yarinyar da magana ma wahala take yi mata, amma ita ce ta zama haka take gaya mata magana. Ramma ce ta hango Abdul yana motsi, ta tashi ta nufe shi da sauri, su Mummy ma suka yi kansa. "Doctor, meyafaru ne? An kira ni aka ce mini ka faɗi" Babban abin da ya ƙular da Mummy bai wuce yadda yake kallon ramma ba, ko ya nuna ya gansu. "Rahama, embassy na Nigeria sun yi iya yin su an shiga an fita, ba za a iya fitar da Daddy ba, za a gurfanar da shi a gaban kotu" yayi maganar muryarsa na rawa. Salati suka saka gaba ɗaya, dan su ba su ma sani ba sai yanzu. Ramma ta riƙe hannunsa ta ce "Ka yi haƙuri Abdul, kowace rai akwai kalar jarrabawar da Allah subhanahu wata'ala yake yi mata, ka yi haƙuri. Mummy ta ɗora hannu a ka ta fashe da kuka, ta ciro wayarta tana dannawa, Jidda na ta ba ta haƙuri, ramma a ranta ta ce "Allah ya ƙara, kaɗan ma ku ka gani, ni kam Allah ya ƙara shirya mini kai ya kare mini kai da ci gaba da aikata duk wani mugun aiki. A zahiri kuma ta ci gaba da rarrashinsa, tana kwantar masa da hankali. ***** Rahila Allah ya taimaketa, aka sallamota daga asibitin masu rangwamen hankali, sai dai duk tayi wani iri, tsufanta ya fito sosai da sosai. Shahida ta zauna ta yi ta mata nasiha a kan tayi haƙuri, ta kwantar da hankalinta, kar ta ɗorawa kanta kishi, idan ba haka ba ta bari Abbu ya saketa ba ta da wurin zuwa ta zauna. Shi kuwa Abbu, hankalinsa ya kwanta, Al'amin ɗin sa ya zama mutum, ya nutsu ya shiryu, ga maman ramma sam ba ta da damuwa da hayaniya, su na zamansu lafiya. Abdul ya takura a asibiti shi a sallame shi, da aka sallame shi su ka koma gida, ko fita baya iya yi, abinci ma sai ramma tayi da gaske yake iya ci. Ta kira mama ta gaya mata, mama ba ta taɓa zuwa gidan ramma ba sai lokacin, suka je tare da Abbu. Duk da da sauran pain ɗin abun da Abdul ya yi musu a zuciyarta, amma sai da ya bata tausayi. Ta din ga jinjina girman ikon Allah, ganin katafaren gidan da rammar ke ciki, komai na jin daɗin rayuwa dai-dai gwargwado akwai shi. Su ka jajanta musu, Abbu ya yi ta yi masa nasiha, tare da nusar da shi muhimmancin addu'a da kuma juriya. **** Nabila kuwa na ta rainon cikinta, da aka raba kayan jauhar, kayan jariran da suka saya, ya faɗo a rabon Nabila, ya tambayeta ta na so ko a sayar a bata kuɗin, ta ce kayan take so. Major buni-buni, sai ya zo gidan Nabila ya dubata, cikin nan yayi girma sosai da sosai. Gaba ɗaya ta zauna a gida ta daina fita, saboda duk wanda ya ga cikin sai ya yi magana. Liti ya saka babansa a gaba, tun da ya ga ya san Major, yake ta yi masa nacin, yaje ya tambayar masa auren Walida, amma babansa yaƙi ya ce sai ya ga kamun ludayinsa sai ya ƙara hankali. Abbu ya samu mahaifin liti ya ce masa shi ne yake tare da su a kasuwa, liti ya yi hankali sosai da sosai, kuma shekarunsa ja suke yi. Da kyar ya amince ya yi wa Major maganar, amma ya yi masa bayanin komai. Major ya ce "Ai ɗanka nawa ne prof, kuma tun da shi ma ya shiryu haka muke so, in dai yarinyar ta na son sa, Ubangiji Allah ya tabattar mana da alkhairi, dama tuntuni  yayarta Nabila ta fara yi mini zancen, idan kun shirya ku zo ayi magana kawai" Liti har gida ya je ya gaya wa Nabila Major ya amince ya bashi auren Walida, tare da ƙara yi mata godiya, bisa ƙoƙarin da ta yi masa. Cikin Nabila na ganin gata, domin kuwa tuni a wannan karon ma Viper ya fara sayayyar kayan jariri, idan ya tambaye ta zaɓi, sai ta ce ita duk abin da ya saya shikenan, ita dai damuwarta ta rabu da cikin nan lafiya. Shahida ce ta fara haihuwa, matar Walid, daga kai ta asibiti cikin dare tana ciwon baya, aka ce ai ta kusa haihuwa, abin har mamaki ya bashi. Viper ba ya gari, Nabila kuma ta yi nauyin da ba za ta iya fita ba, Walid baki yaƙi rufuwa, wai shi ne ya zama uba, Allah ya bashi ɗa namiji. Liti har ya fishi murna, kamar ɗansa, ya din ga bin sa yana cewa "Saura ka saka masa sunan Viper, alhalin gani, sunana zaka saka masa" "Kai a wa?" "Ni a baban yaron mana, dan Allah Walidi ka saka masa sunana Abdallah, na san rashin m ɗinka, tsaf zaka saka masa sunan Viper, dan muraran ka ke nuna fifikon ka fi son sa a kaina" Kafin suna Viper ya zo gari, Nabila ta so ta bishi ta je ta ga yaron, amma ya ce ba zata fita a din ga tanka ta ba. Viper kamar ya tafi da yaron, ya din ga addu'a Allah ya nuna masa na sa haka shi ma. Yayi masa addu'a sosai da sosai yaron. Walid ya sanya sunan mahaifinsa Umar. Dubu ɗari Viper ya bawa Walid, ya ce masa yayi haƙuri, abubuwa ne sun yi masa yawa. Yanayin jikin Nabila, ya sanya Major ya tura Baba magajiya ta zauna da ita. Sai dai idan Viper yana nan 'yar kallo take zama, sai dai ta yi ɗan aikace-aikacen gida. Hatta wanka sakata yake a toilet ɗin ƙurya ya wanketa, undeas ɗin ta, idan ta cire duk shi yake wanke mata. Shi kansa ba ƙaramin tausayi take bashi ba, idan ta zauna shi ma cikin nasa zaman yake yi. Zama sai da dabara, tashi sai da dabara, haka bacci ma, gashi tun da ya ƙara tsufa, take fama da matsalar numfashi, dan ma ba ta da yawan complain, sai dai shi ya fuskanci akwai matsala. Sanin alaƙar da take tsakanin Sumayya da Nabila, ya sanya mijinta ba ya damuwa, da yawan zuwa gidan Nabila da take yi, duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata. Duk shagwaɓa da rigimar Nabila idan ba ta da lafiya, yanzu babu, sai dai idan an yi mata sannu ta yi murmushi kawai, gaba haka kurum take jin ta sare, kamar mutuwa za ta yi idan ta zo haihuwa. Duk da ita ce abin tausayi, amma tana tausya wa Viper sosai da sosai, bawan Allah sai ya zauna ya zuba mata ido, duk motsinta tausayinta yake ji, da ta motsa zai tambayeta me take buƙata, me take so. Har nauyinsa take ji, ta ce tana buƙatar wani abu. Ana haka mama uwargidan baban su Nabila, Allah ya karɓi rayuwarta, duk unguwa ba in da zancen jinyar wulaƙancin da 'ya'yanta su ka yi mata bai je ba. Nabila tana ji tana gani, babu roƙo da magiyar da ba ta yi ba, Viper ya ce sai dai ta yi addu'a daga gida, ba zata je ko ina ba. Mutuwarta ta ƙara razana Zakiyya, ta din ga ganin saura ita. Watan jaririn Walid biyu, Nabila ta fara naƙuda, tun cikin dare suka tafi Asibiti, amma har garin Allah ya waye ba ta haihu ba. Tun da aka gaya wa Major da sassafe sai gashi a asibitin, ya zo ya tarar da su da Viper da baba magajiya, an fito da Nabila tana zagaya wa, ta samu wuri ta zauna a jikin Viper saboda ta gaji da zagayen. Viper na gaida shi, amma bai ji ba, hankalinsa na kan Nabila, ya riƙe hannunta ya ce "Sannu Arfa na, ya jikin?" "Da sauƙi Abba" "Allah ya rabaki da cikin nan lafiya, ki ci gaba da addu'a kin ji, muna taya ki" Ta jinjina masa kai, mai haɗe da yaƙe. Duk wanda ya wuce ya ga Nabila, sai ya sake waiwaiwayawa ya kalli cikin nan. Shahida ta kira wayar Nabila, dan tun yammacin jiya ta kirata take tambayarta, wai ya mutum yake gane naƙuda yake yi. Viper ne ya ɗaga ya sanar mata su na Asibiti. Shahida ta gaya wa Walid, lokacin bai fita kasuwa ba, ya cewa liti ya wuce kasuwa, zai fara biyawa ya duba Nabila, liti ya ce "Saboda ka rigani ganin ɗan mai zamani ko? To baka isa ba" A asibitin suka haɗu, Walid jikinsa yayi sanyi, dan bai manta yadda Shahida ta din ga fama ba. Liti ya zata abin wasa ne, ganinsu a zaune a harabar wurin a kan kujera, har tana shan shayi. Wata Nurse ta fito ta ce mata ta daure, ta tashi a mayar da ita labor ward a sake dubata. Da Nabila ta miƙe sai da gaban liti ya faɗi, tare da mamakin yadda aka yi tayi rayuwa da wannan cikin, duk da da hijjabi a jikinta. Su na tafe idan ciwon ya motsa sai ta rirriƙe Viper, tana yarfa hannu tana ambaton Allah. Liti ya ce "Walid gaskiya tafiya zan yi, idan ta haihu ka kira ni a waya,na ci gaba da zama a nan kuka zan yi, wallahi na zata haihuwar ba wahala" Walid zai yi magana ya ga da gaske hawaye ne a idon liti, wanda liti da bakinsa yake cewa shi fa sai a shekara ko ƙwalla bai yi ba. Wasa-wasa har Baba sai da ya zo asibitin, Nabila ba ta haihu ba, Viper ji yake kamar ya tayata ciwon, tun da cikin nan ya samu a wahala take. Idan ta gaji, sai ta fashe da kuka, sai dai Viper ya yi ta rarrashinta, yana ba ta haƙuri. Har sai da ya cewa Abdul, ko ayi mata tiyata kawai. Abdul ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri, lokaci ne zata haihu da kanta in sha Allah, haka kowace mace take ji. Babu tangarɗa a laborn dan haka a ƙara haƙuri. Sai da ta kusa daf, sannan aka ce Viper ya fita waje, ya din ga sintiri a bakin ƙofa, yana addu'a, sai dai ya din ga tuna Jauhar, yana fargabar Allah ya sa kar wani abu ya samu Nabila da yaran. Doctor Abdul Yasar, ma'aruf Indabo, shi ya karɓi haihuwar Nabila, ta sha wahala sosai da sosai. Dan bayan da jaririn ya faɗo, sai da ta kuma wani ciwon sannan ta biyun ta faɗo. Hamdala ta din ga yi, tana yi wa ma'aikatan godiya, saboda gudunmawar da su ka bata. Abdul ya ɗora mata jariran a kan ƙirjinta, ta rungume su, kawai ta fashe da kukan murna. "Ya haiyyu ya ƙaiyyum ya zuljalalu wal ikram, ya Ubangijin Al'arshi ya Allah duk mai neman haihuwa in dai alkhairi ce , Ubangiji Allah ka bashi yara masu albarka, Allah ka bashi yara masu jin ƙai ababen alfahari ga addinin musulunci, Allah duk mai nema ka bashi, kamar yadda ka azurta Annabi Zakariyya Alaihissalam a lokacin da ya roƙeka. Allah na gode maka da wannan ni'ima, Allah ka raya mini yarana, ka shirya mini su" Su ka din ga amsawa Nabila da Amin. Viper ne kaɗai a wurin da labor room yake, su Major su na can waje. Nabila ta sha ɗinki ciki da waje, ta ji yadda gaba ɗaya ɗakin ya cika da ƙarnin ƙazantar haihuwa, amma daga Abdul har Nurses ɗin, babu wanda ya nuna ƙyamar sa a gareta. Aka shirya yaran tsaf, ita ma aka shiryata, ya basu wuri, nurses ɗin suka ƙarasa taimaka mata, ta shirya, aka yi mata allurai aka fito da ita. Aka wuce da ita postnatal room, ana miƙo wa Viper yaran, amma bai bi ta kansu ba, ya nufi in da aka shiga da Nabila. "Abla" ya kira sunanta. Ta ɗago idanunta da suka yi jawur saboda wahala, ga bacci tana ji. Rungumeta ya yi yana shafa kanta ya ce "Sannu my love, Ubangiji Allah ya yi miki albarka, ya dauwwamar da farinciki a rayuwar aurenmu" Cikin shagwaɓa ta ce "Vi na sha wahala" "Na sani sweetheart, na gani, sannu Abla. Alhamdilillah ala kulli halin. Na gode, na gode my world" yayi maganar yana sumbatar goshinta. Hannunsa ta riƙe ita ma ta ce "Ni na gode da kasancewa tare da ni, ba tare da ƙosawa thank you very much" ya riƙe hannun nata sosai ya ce "Lokacin Jauhar na raye, ta din ga ce mini tsoro take ji, tana son na kasance da ita lokacin haihuwa. Allah bai amince ba, ban kasance da ita ba, amma na cika alƙawarin da na yi mata a kanki" Nabila ta yi murmushi ta ce "Na yi mata addu'a sosai da sosai, Allah ya jiƙan 'yar madararmu" "Amin my love" Abdul ne ya shigo da jariran a hannunsa ya ce "Wai ba kwa san yaran ne? Ana ta rawar ƙafa a baka su, amma ka ƙi kallonsu, ga su nan an yi musu rigakafi, BCG da HB kafin mutane su fara zuwa ɗaukar su" Viper ya yi murmushi ya ce "Sun wahalar mini da mata, shiyasa na ɗan yi fushi, amma tun da tana nan ƙalau, barakallahu fihum" yayi maganar yana karɓar su, cikin wani irin maɗaukakin farinciki mara misaltuwa. Abdul ya ce  "Wannan boss ɗin da kai yake kama, fuskarka ce wannan" Viper ya yi dariya. Su Major ne su ka shigo, shi ma sai da ya fara nufar gadon Nabila, ya tabattar tana lafiya. Kan ka ce kwabo, Asibiti ya ɗinke da mutane, 'yan barkar Nabila. Da liti ya zo duk jikinsa a sanyaye, ya din ga jerawa Nabila sannu, halin da ya ganta a ciki ɗazu, ya ƙara sanya masa tausayin mata. Ya ja gefe aka miƙo masa jarirai. Bai san lokacin da ya ce "Kan uba, kumbo, Viper wannan fuskar ai taka ce, ka ga jariri yadda ya haɗe fuska kamar zai kai duka. Allah ya baki juriyar tarbiyya, wannan zai yi taurin kai kamar babansa" Ba wanda bai yi dariya ba, macen ce take ta tsotsar hannunta, tana buɗe idanunta tana lumshe su a hankali. "Allah ya raya mana ke 'yar madara, Allah ya sa ki ɗaukko halin mai sunanki" Viper ya ce "Har ka saka mata suna?" "Eh gaskiya, na saka mata suna fatima zahra, 'yar madara" Viper ya yi murmushi ya ce "Babanki ya saka miki suna, Allah ya raya ki bisa tafarkin addinin musulunci" Bayan awanni shida aka sallami Nabila, gida ma da suka tafi, ana ta zuwa barka. Washegari hafsa su ka zo Kano da Hafsa, Hafsa kamar a bar mata jariran nan. Alhaji mu'azzam ya ce "Wannan dai na san 'yar madara ce, shi kuma ogan fa ya sunansa". "Takwara na yi muku kai da Abbu, Ibrahim ace masa mu'azzam ko Khalil" Ita kanta Nabila ba ta zaci haka zai yi ba, ta ɗauka sunan Nura yayan ramma zai saka" Alhaji mu'azzam bai taɓa zaton Viper zai yi masa kara haka ba. "Masha Allah, amma na gode sosai da sosai, idan ina da rabo nima Allah ya bani ɗa namiji, Allah ya raya khalil" Viper ya ce "Mu ke da godiya, har duniya ta naɗe, ba zamu taɓa manta abin da ka yi mana, Allah ya saka da alkhairi" Kankarofi ya ce "Kar ka damu Viper, yi wa kai ne" An sha shagalin bikin suna sosai, Alhaji mu'azzam ne ya yi wa jariran Viper hakika, sun samu tarin kyaututtuka, ta in da suka zata da in da ma ba su zata ba. Sai dai Nabila ta fara fama da ɗawaniyar raino, Khalil ba shi da afuwa wurin tsotsotso, 'yar madara ba ruwanta idan an ba ta ta sha, idan ba a bata ba, sai tayi ta tsotsar hannunta. Viper ya ce "Ba fa zai yiwu ka hana mini 'ya kumari ba" Haka zai tsigo shi daga jikin Nabila yana tsala kuka, ya bata 'yar madara ta shayar. Baba magajiya ce take yi wa Nabila wankan jego. Watan Nabila ɗaya da haihuwa, aka yankewa Indabo hukuncin kisa a ƙasar saudiyya. Ko a iya haka Viper ya ɗan ji sanyi a ransa, duk da ba za a taɓa wanke masa zuciya ba, haka ma maman ramma. Bunkure kuwa ana ta jan shari'ar ta, saboda tuhume-tuhumen da ake yi mata da yawa. Abdul ya sha tashin hankali, saboda yadda maganar kashe Indabo ta karaɗe ko ina a ciki da wajen ƙasar nan. Nabila ta fara mayar da hankali a kan ƙoƙarin ta, na fito da hanyoyin taƙaita shaye-shaye, a tsakanin al'umma. Ta fara da rubutun ƙanan litattafai, masu ɗauke da zane-zane, da suke ankarar da illar shaye-shaye da 'yan makaranta tun daga primary zuwa secondary za su iya amfani da shi. Aka gudanar da babban zaɓe na ƙasa, gwamnati ta canza bara gurbi daga cikin muƙarabbanta, yayin da Alhaji mu'zzam ya ɗare kujerar sanata. Jidda babu yadda ba ta yi ba ta koma gidansa, amma yaƙi. Zakiyya kuwa sai abin ya zame mata ga bikin zuwa babu zanin ɗaurawa, ga kuɗi iya kuɗi hafsa na cikin daula, amma bata nutsuwar ƙwaƙwalwar da za ta ci, kullum a zabure take cikin tashin hankali. Ba a rufa watanni uku ba, shugaban ƙasa ya rattaɓa hannu, a kan sauya shugabannin da za su jagoranci rundunonin tsaro na Nigeria. Viper mamaki ne ya cika shi, ganin matsayin da aka ɗauka aka ba shi. Sumayya gwamantin kano, ta buƙaci su yi aiki da ita, ayi mata S.A daga ita har Nabila, amma suka ƙi hakan, saboda ƙungiyar da suke son kafawa, ba sa son siyasa ta shiga ciki, su na so tayi hannun riga da irin ta bunkure. Nabila ta fito daga wanka ta na shirya, ta tsaya tana kallon kanta a mudubi, Viper yana ta rarrashin Khalil yayi bacci, ya ga ta tsaya ta yi shiru tana ƙarewa jikinta kallo a mudubi. "Madam ya dai?" "Vi, kalli duk na yi wani iri, kalli tumbina yadda yaƙi komawa gaba ɗaya, kalli stretch marks duk ya ɓata mini jiki, kalli yadda cikin yayi, kalli breast ɗi na ma, duk stretch marks, ni Allah ya sa kar su yi sagging ma idan na yaye su" tayi maganar cikin damuwa. Ya tashi ya ƙarsa in da take, ya tsaya a bayanta, yana kallonta ta jikin mudubi. Ya zagaya hannunsa a cikinta, yana shafa cikin a hankali ya ce "This is motherhood abla, yara biyu ne fa suka kwanta wata tara a cikinki, ta yaya ki ke expecting ki zauna a yadda ki ke?" "Vi zan daina yi maka kyau, kalli tumbina fa, ji nankarwa, kalli breast ɗina, duk yadda ya cika maybe da na yaye su ma zubewa za su yi" Ya kwantar da kansa a kafaɗarta ya ce "Idan na ce zaki daina yi mini kyau, ban yi wa kaina adalci ba ko kaɗan abla. Ba zaki taɓa komawa yadda ki ke a da ba, kar ki damu kanki, ki ce sai kin yi abin da zai cutar da ke, sai nankarwa ta tafi, sai breast ya koma yadda yake a da, ban ƙi ba ki yi gyara, amma ban da cutar da kanki, ki yi alfahari da wannan nankarwa tambarin zama uwa kenan, ni kyau take yi mini ma, ba na cikin mazan da zan damu da sauyin da jikin matata ya samu, alhalin na san ba a haka na aureta ba, dan duk wanda yake a haka, zai zama mai yawan zalama da hange kuma ba zai taɓa samun yadda yake so ba. Ina sonki a duk yadda ki ke ablana, ni kullum mai kyau ce ke a idona." Juyowa ta yi suka rungume juna tana murmushi, ko ba har zuciyarsa yayi maganar nan ba, ta ji daɗi a ranta, balle ma Viper da ba ya abu dan a so shi, idan abu bai yi masa ba faɗa yake yi. A lokacin da aka shirya walimar karrama Viper, ɗan mama ya zo, Liti ya rungume shi cikin murna da farinciki ya ce "Ɗan mama kai ne ka zama haka? Ni da tsulai, kai in da aka kai kan, tsotsarka suke yi ne, ka ga yadda ka koma kuwa? Ni da takanɗa" Ɗan mama ya ce "Oga liti kenan, ai gara ace garin mayu aka kai ni, ake lasata da azabar da ake gana mini" Kamar Liti ya haɗiye ɗan mama dan murna, har Abdul sai da yaje wurin walimar nan, a ransa yake ta ƙara jinjina lamarin Allah, ɗan daba mara galihu, yau ya zama daga cikin manya a jami'an tsaro. Ramma da tsohon ciki ta kammala WAEC ɗin ta, sun gama babu jimawa ta haihu, ta haifi ɗa namiji, ana haifarsa Abdul ya ce Nuradden ya saka wa jaririn. Ba ramma ba hatta mamanta, sun ji daɗin abin da Abdul ya yi. Mamansa dole ta zubar da makaman adawa da ramma, ganin kaf iyalinta sun tarwatse, sai Abdul, shi kuma ta matarsa yake yi, a dolenta ta sassauta ƙiyayyar da take yi mata, mussaman da ta haifi Nuruddeen. Viper ya ba wa jaririn kyaututtuka daban-daban. Bayan yi wa Viper ƙarin girma, sai da aka bashi motar hawa, da gidan zama. Abin da ya fara yi, ya je unguwar su, ya samu mai unguwa aka zauna da manyan unguwar, ya ce a tattara masa duk yaran da suke harkar daba, waɗanda suke da sha'awar aikin soja, a ɗauki sunansu a bashi. Sannan a duba mutum biyar, za a kai su kasuwa, wurin su Walid, masu son komawa makaranta ma, a ɗauki sunayensu, a kai wa distinguish senator Mu'azzam kankarofi, a ga ta ina za a taimaka musu. Amma duk wanda aka samu da cin amana, sai ya ɗaure shi, kuma babu wanda ya isa ya karɓe su, bisa yarjejeniya za a rubuta komai. Ya haramta daba a yankin unguwar da kewayenta, ko dai mutum ya rungumi zaman lafiya, ko kuma zai ɗauki matakin da ya dace a kansa. Major bai saka lokaci mai tsawo ba, na auren Walida da Abdallah, liti kamar ya janyo lokacin mussman idan ya ga 'ya'yan Viper da kuma na Walid. Khalil rigimamme ne, baby jauhar kuwa babu ruwanta, bayan nono da madara ake haɗa musu, saboda shayarwar na ba wa Nabila wahala, Khalil kaɗai idan ya sakata a gaba, sai ta fara jiri. Nabila ta dage a kan ƙungiyar ta, da gaske take son yaƙi da daba da shaye-shaye, tare da yaƙi da bangar siyasa. Tare da sumayya suke faɗi tashin su, ta hanyar amfani da kafafen sada zumunta da kuma kafafen watsa labarai, wurin bayyanar da manufar su. Suka samu goyon bayan manyan lauyoyi, da 'yan jaridu, Nabila ta na yawan nanata su ƙungiyar su ba ta siyasa ba ce ba, kuma ba ta gwamnati ba ce ba, dan haka duk ta kan wanda aiki ya biyo za su yi aikinsu ne, ba tare da sani ko kuma sabo ba. Ta kuma samu cikakken goyon bayan mijinta Al'amin, ɗari bisa ɗari. Tare da amincewar gwamnati, aka bibiyi rubuce-rubucen da ta yi, aka yi gyare-gyare, aka fara rarraba su kyauta a cikin makarantu, wanda suka haɗa har da ƙanan labarai, masu kama da tatsunuyoyi, wurin nuna illar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da bangar siyasa. Haka nan mawaƙa sun bayar da gudummawa, wurin waƙoƙin yara, da suke nuni da illar waɗannan miyagun ayyukan. Misalin ƙarfe takwas na dare, Viper yana zaune a katafaren falonsa, za ayi hira da Nabila, a babbar tashar talabijin a Kano, kuma Sumayya ce za ta gabatar da program ɗin. Khalil sai tsalle-tsalle yake yi, ya faɗa nan ya tashi can, kamar ɗan aljani. Jauhar kuwa na jikin Viper a kwance, tana ta tsotsar hannunta. Viper ya fi shiri da 'yar madara, babu ruwanta, ba rigima ba rikici, ga ta da haƙuri, Khalil kuwa ɗan gidan Nabila ne, ita kaɗai take iya masa, ba ya ji ko kaɗan, ga wasan kasada, duk wani wasa da zai yi ya cutar da kansa shi yake yi. Ga miskilancin tsiya da kukan banza, gashi abu kaɗan Jauhar za ta yi masa ya maketa, ko ya cijeta. Sai dai idan Viper ya gani, ya murɗe masa kunne, ya tafi wurin Nabila yana kuka. Yanzun ma Viper ne ya kalle shi, yana ta hawa kan kujera yana dirowa da ka. "Ko ka zauna ka bar abin da ka ke yi, ko kuma ka fita, maminku ce za ta yi program zan kalla" Da sauri ya saukko ya zauna a ƙasa ya ce "Mamina ce nikaɗai" "Eh an ji taka ce, ni ma jauhar ɗi na ce nikaɗai" "A'a daddyna ne" "A'a kai ɗan mami ne, ni kuma 'yar madara ce tawa" Tasowa yayi yana kuka yana cewa "Daddyna ne, mamina ce" shi ma ya zauna a jikin Viper" Jauhar ta sake gyara kwanciyarta a jikin Viper, ba tare da ta kula Khalil ba. Fara program ɗin ya sanya, gaba ɗaya suka mayar da hankalinsu kan TV. Bayan gabatarwa, Sumayya ta tambayi Nabila, menene dalilin da ya sanya ƙungiyar ta, ta fi mayar da hankali a kan harkar daba da shaye-shaye, da kuma bangar siyasa?" Nabila ta ce "Saboda tun da ake yi, bamu taɓa cin ribar abin ba, sai koma baya, da kuma lalata goben matasanmu, lalacewar goben matasa kuma lalacewar al'umma ce" "Ta yaya? Kuma wasu hanyoyi ki ke ganin za a bi a magance wannan matsalolin da ku ka sako a gaba" "Saboda su ne shugabanninmu na gobe, waɗanda za su jagoranci al'umma. Muddin bangar siyasa abin arziki ne, yan siyasarmu ba za su nemi ɗan talaka yayi musu ba, 'ya'yansu za su ka su yi musu. Meyasa ba sa kai yaran talakawa, ƙasashen waje su yi karatun injiniya lauyoyi, likitoci da makamantansu, ko kuma ɗan talaka ba shi da ƙwaƙwalwa da zai yi ilimi ya zama likita, ko injiniya?. Hannu ɗaya baya ɗaukar jinka, kuma hannu da yawa maganin ƙazamar miya. Dole ne iyaye, malamai, gwamanti, hukumomi, mu haɗa hannu mu kawo ƙarshen shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da kuma bangar siyasa. Mu ba wa yaranmu kulawa da ilimi kamar yadda Allah ya ce mana masu kiwo ne mu, kuma ababen tambaya a kan kiwon da aka bamu. Kar ka haifi ɗan da ba zaka iya ɗaukar nauyinsa ba, dan jin daɗinka kawai. Sannan iyaye su din ga bawa hukumomi damar hukunta yaransu, a duk lokacin da aka masu da laifuka. Sannan su kansu hukumomin da 'yan siyasa su ji tsoron Allah, wurin kama masu laifi, da sakinsu ba bisa ƙa'ida ba. Babu wanda ya taɓa zama wani abik alfahari, a dalilin ta'amalli da miyagun ƙwayoyi. Ba hujja ba ce matashi ya zauna ya ce sai gwamanti ta bashi aikin ba shi da aikin yi. Masu kuɗin duniya babu wanda yayi kuɗi da aikin gwamnati. Ina kira da matasa, ku tashi ku nemi na kanku, ku nemi ilimi, duk wanda ku ka zaɓa, bai yi muku abin da ya dace ba, ku ɗaura ɗambar dawo da shi, ta hanyar recall election, ko  kuma ku canza shi a lokacin zaɓe. Kuma za ku iya zama likitoci, injiniyoyi da makamantansu, ku ba bayin 'yan siyasa bane ba, da za su yi amfani da yau ɗinku, su lalata gobenku, domin ku dauwwama ku na yi musu bauta da yaransu. Su daina ba ku miyagun ƙwayoyi, ku na sha ku na kashe kanku, alhalin sun kauwwame yaransu, sun tura su in da za su yi ilimi, sun kwashe dukiyoyinku sun tara wa iyalansu arzikin da ba za su yi talauci ba, sun bar ku da bauta musu, da zubar da jininku yadda suke so, alhalin iyalansu su su ka fi cancanta su yi musu wannan aikin ba ku ba. Ina fatan nan gaba kaɗan in ga matasa 'yan shekara talatin zuwa ƙasa a majalissu, in gansu a cabinet ɗin shugaban ƙasa. Mu ga matasa ɗanyen jini, sun gaji manyan malamanmu, irin su marigayi Albani zariya, Sheikh ɗahiru usman bauchi, dr. Isa Ali Ibrahim fantami, malam umar sani fagge, malam Aminu Ibrahim daurawa, malam Ahmad guruntum, Sheikh Ahmad bamba rahimuhullah, malam Nasiru kabara. Ina fatan na ga mun samu ire-iren ɗangote da dama, in ga natasanmu sun zama dactoci da profesoshin ilimi da duniya za ta yi alfahari da su. 'yan daban nan 'ya'ya ne, kuma za su amfani al'umma idan aka tsaya wa rayuwarsu" Sumayya ta ce "Sannu da ƙoƙari, kin kwararo bayanai, masu matuƙar ma'ana, kin ƙara ƙarfafa mini gwiwa, kamar na fito takara nima, duba da yanayin lokaci, bari mu waiwayi masu sauraro, mu ji gudunmawar da za su bamu" Bugowar farko, muryar Viper ta yi amsa kuwwa a cikin wayar tarhon. "Ina yi wa baƙuwa barka da zuwa, haƙiƙa ta yi bayani masu ma'ana, amma tayi tuya, ta manta da albasa, ba ta tofa komai a kan iyaye mata ba" Murmushi Nabila ta yi, domin kuwa muryar Khalil ta jiyo yana kiran mami ta cikin wayar. "Mata iyayen al'umma, mata iyayen giji, a basu ilimi, a kula da su, kar ayi musu fyaɗe a ɓoye, domin gudun zubewar mutunci, a ƙi ɗaukar musu mataki, kar a ɗora musu talla, kar a tura su barace-barace, kuma kar ayi musu auren dole, kar a zalunce su. A wadata su da ilimi, a tausaya musu a ba su damar cika burikansu. Babu wata mace da zata iya rayuwa ta tsaya da ƙafarta, ba tare da ta jingina da namiji ba. Kamar dai ni, babana ya share mini fagen cikar burina, mijina kuma ya bani dama kuma ya tsaya mini, hakan baya nufin lalacewar macen. Ni 'ya ce, matar aure, uwa kuma lauya mai zaman kanta, ina fatan nan da shekaru kaɗan na ga mata ire-irena sun yawaita, kuma matasa sun kama hanyar gyara rayuwarsu, domin samar da kyakykyawar gobe ga al'umma da ƙasata baki ɗaya." Nabila ta sha tambayoyi daban-daban, kuma sosai ta ƙara zaburar da al'umma, mutane da dama su ka nuna sha'awar su, a kan ƙungiyar, sai dai ta nanata cewar ƙungiyar ta ba ta siyasa ba ce ba, kuma ba ta neman kuɗi ba ce ba. Hankalin Nabila ya kwanta sosai da sosai, Allah ya dafa wa lamarinsu, ga Alhaji mu'azzam sosai yake tallafawa matasa, yake tafiya da su, tare da bankaɗo masu ilimi da himma a cikinsu, ya samar musu aiki, da sama musu appointments a ƙasa. Kankarofi na daga cikin yan majalisa da suka kawo wa yankin arewacin Nigeriya cigaba sosai da sosai. Liti tuni ya angwance da Walida, cikin ikon Allah kuma ya rage rawar kai, saboda daraja da kamala ta aure, da ta hau kansa. Bayan shekaru uku, Abbu ya basu damar tsayawa da ƙafafuwan su, ta hanyar ba su jari aro, da kuma kama su musu wurin gudanar da sana'a. Nabila sai da ta haifa wa Viper yara biyar, sau biyu tana yin twins, sai kuma Namiji a tsakiya guda ɗaya, sai dai Khalil shi ya ɗaukko halin Viper gaba ɗaya babu abin da ya bari. Abdul ya tsaya wa ramma, sai da ta zama cikakkiyar Nurse, shi ma ta hayyafa sosai da shi. Rahila daga baya Allah ya yi mata rasuwa, jikinta yaƙi daɗi haka ta koma ga Allah. Hafsa kuwa haihuwar dai Allah bai bata ba, amma Kankarofi ya zauna da ita cikin mutuntawa da so da ƙauna. Daga Walid, liti, Viper ɗan mama, idan aka ce sun yi daba a baya, idan ba wanda ya sani ba, sai ya ƙaryata. Viper sai da ya kai Nabila, wurin maƙwabtan Jauhar da suka yi zaman amana da ita a unguwar da suka zauna. Viper ya riƙe muƙamai da dama, a gidan tsaro na soja, gefe guda yana kasuwanci. Ƙungiyar Nabila ta taka muhimmiyar rawa sosai da sosai, a kan canza tunanin mutane da dama. *TAMMAT BI HAMDILLAH* 1/8/2024-20/12/2024 *DUKKAN YABO DA GODIYA DA JINJINA DA KIRARI, SU TABATTA GA UBANGIJI MAƊAUKAKIN SARKI, UBANGIJI TALIKAI BUWAYI GAGARA MISALI, DA YA BANI ARON RAI DA LAFIYA NA FARA WANNAN LITTAFI LAFIYA NA KAMMALA LAFIYA* JINJINA GA ƘUNGIYAR MIKIYA WRITER ASSOCIATION BRIGHT PENS TEAM Nazeefa sabo Nashe Zee kumurya Na'aima Suleiman sarauta Aisha Adam Ayshercool GAISUWA TA MUSSMAN GA Mahaifiyata malama Nafisa Adamu Muhammad Mahaifina malam Adamu Yakubu GODIYA TA MUSSMAN GA Adamu Adamu Yakubu ASP Ibrahim Na'ibi Barrister Amina Aliyu Barrister Ibrahim Jinjina da gaisuwa ta musamman, ga kafatanin al'ummar da suka kasance da ni, a wannan littafi. Iyayena, kakannina, yayye ƙanne da sauransu, masu gyara, masu sharihi, da masu bayar da shawara ina godiya sosai da sosai. 'yan comment section, Alkhairin Allah ya kai muku. Na so kama sunaye, amma na san dole zan manta da wasu, kafataninku ina godiya Allah ya saka da mafificin alkhairi. Abin da na rubuta na daidai, Allah ya sa al'umma su amfana, akasin haka kuma ina fatan Allah ya yafe mini, kuma ya sa al'umma su yi watsi da shi. Waɗanda na ɓata wa rai kuma, ina fatan ku yi mini afuwa, hada-hadar jama'a pressure da yawa. Albishir na musamman ga kafatanin waɗanda su ka bibiyi littafin *ƘARFE A WUTA* Na san ku na cike da kewar kammala karatun labarin Viper, labari mai cike da ilimantarwa, faɗakarwa da nishaɗantarwa, to ga sabon Albishir, littatafai uku, cikon *BRIGHT PENS SECOND BATCH* litattafan da za su maye muku gurbin labarin ƙarfe a wuta. *MUTALLAB* (Mallakar Nimcyluv) *HADARIN GABAS* (Mallakar Nazeefa Nashe) *ZAYTOON* (Mallakar zee kumurya) Ina da tabbacin yadda ku ka ji daɗin ƘARFE A WUTA, ba zaku yi dana sanin labaran nan uku ba, da su ka fito daga team ɗin *BRIGHT PENS* Domin neman ƙarin bayani, kai tsaye ku na iya tuntuɓar waɗanan lambobin. 0904 787 1750 0816 406 9385 Alhamdilillah ala kulli halin. Domin gyara, sharhi ko shawara Ayshercool 08081012143