Compiled By Umar Dalha Funtua. *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM!._* 👉🏻1⃣ *Matsanan cigar* hayaniyar dake tashi agidan ce taja hankalina, cikeda bak'in ciki natashi daga barcin safen dana koma, fitinar gidanmu dabance data kowane family House dana Sani kona ta6a jin labarinsa a rayuwata, haka gidan namu yake kullum tamkar kasuwar 'yan danbe, daga matan gidan zuwa 'yan mata da yara tamkar muna ganin hanjin juna, saika rantse badaga tsatso d'aya muka fitoba. Kururuwar danaji maman Safara'u ta kurma yasani kuma jan dogon tsaki, sai kuma najiyo muryar gwaggon haleema Na fad'in “kai amma wannan lamari baiyi dad'iba, kekuwa maman biyu ya kamata ki canja wannan halin naki, dan tabbas inba wani abu kikayiba babu yanda za'ayi yaronan Sadeequ yadage shi cikinsu *MUNAYA* yakeso, duka yaushe aka gama maganar nan akan shafi'u amma shine zaki koma kan Sadeequ kuma yanzu?”. gaba nane ya fad'i, cikin zaro idanu waje nace, “ashema mu akanmu fitinar take yau?”. yink'urin sakko nake daga gadon Munubiya tashigo tana share kwalla, binta nayi da kallo harta fad'a saman gadon ta kwanta rufda ciki tareda fashewa da kuka mai ban tausayi. Hakan Yakuma tabbatar min lallai mud'inne dai ake hargowar akanmu. a fusace Na dirgo daga gadon na nufi k'ofar fita, (ko kad'an banida hak'uri, musamman akan cin zarafin mahaifiyarmu da akeyi agidan lokuta da dama idan irin hakan ta taso), taku biyu nayi naji an damk'oni, najiyo cikin masifa dan nasan Munubiya ce. “wlhy ki sakeni kafin nafara huce haushina akanki munu! yau saina gyarama kowacce 'yar iskar mata zama agidannan dan kutu..... Bankai ga k'arasawa ba Munubiya tai saurin rufe bakina da tafin hannunta. Kici-kicin kwacewa nafarayi amma nakasa, dan bak'aramin ruk'o taminba, raina yak'ara 6aci ainun danjin irin rashin kunyar da Safara'u ke zubama innarmu a tsakar gida, bansan na wancakalar da Munubiya gefe ba nafice da gudu. Babu Wanda yaga fitowata sai dai saukar sautin marin dana zubama Safara'u a farar fuskarta sukaji. Hakan yaja gidan yay tsit na wucin gadi, sai kuma hayaniya takuma 6allewa, Safara'u da mamarsu sukayo kaina danufin duka.... Tsawar da baba k'arami ya bugace tasaka kowa dakatawa tsakanin ni dasu, hakama matan gidan sai suka fara jan k'afafu danufin barin wajen. A tsawace yace, “kar wadda tabar wajen!!”. Tsitt kakeji gidan yayi, tamkar bashi bane d'azun ya cakud'e da hayaniya tamkar ana biki ko suna. Jarabar gidanmu ba bak'on Abu bane a anguwarmu, danta rigada tazama tamkar ajininmu take (yo ajininmu mana zance) tunda kullumne babu fashi sai anyi hayaniya, kodai matan gidan kokuma mu 'ya'yan gidan. Babu mai d'agama wani k'afa koda na second d'ayane kuwa, yanzun zakaji gidan shiru, anjima k'ad'an kaji an doka gangar shaid'an, musamman ma fad'an yara dayafi komai saurin had'a fad'an matan gidan da a kulum, a rana sai ayi fad'a biyar akan yara kawai, innarmu ce kawai da Maman Fauziyya keda k'ok'arin K'aucewa irin wannan fitintunun dasuka zama tamkar shan ruwa acikin gidanmu. Baba k'arami yafara fad'a tamkar zai ari baki, inda yake shiga bata nan yake fitaba, kowa yayi tsit yana saurarensa, (saboda kasancewar masifaffe shima) sai da yayi mai isarsa sannan yajuya yafita yana fad'in nida Safara'u mu sameshi falonsa. harda iyayenmu mata. Duk abinnan da akeyi innarmu na kicin tana had'a Karin kumallon safe, kuma kalma d'aya bata tofaba a zancen nasu, datasan ma zan fito bazata barniba nima. A falon baba jafaru yanemi jin ba'asin tushen fitinar, cikin d'aga muryar da hargowa maman Safara'u tafara fad'in “Alhaji wlhy kashiga tsakanina da maman biyu a gidannan, idanfa tanama sauran matan gidannan Yanda taske so, suna barinta nibazan bartaba, tasanni tasan waye ubana ehe, kum....... Hannu yay saurin d'aga mata, “kinga Suwaiba nifa ba wannan ne yasani kiranku ba, sonake naji minene ya kawo hayaniyar?”. Cikin jin haushin an tareta tace, “Alhaji akan yaronnan Sadeequ ne, kowa yasan wajen Safara'u yake zuwa a unguwarnan, amma jiya da yamma sai ya aiko kiran Munaya, dayake ALLAH yatashi tonon asirinsu sabida bayaune na farko ba sai d'an Aiken ya kwatsa maganar a tsakar gida, babu dai Wanda yace komai, dan azatonmu ba Sadeeq d'in Safara'u baneba, goshin magriba saiga Safara'u tashigo tana kuka. Na tsareta da tambaya da k'yar tacemin cikinsu 'yan biyu tagani da Sadeeq a zauren gidan Malam halilu suna hira da dariya, kuma hardama mata gwalo akayi. Saboda na gaskata zancenta na sake aiken Rahma taganomin da idonta, harma taji Sadeeq d'in nafad'in ai koma miza'ayi bazai auri Safara'u ba, cikin wad'an nan munafukan yaran daba ganesu akeba zai aura, saboda darene yasani d'inne maganar a raina har safiyar yau d'inan, amma wlhy Alhaji da k'yar na iya barci nida Safara'u jiya. “hummm” kawai nafad'a ina dafe kaina, saboda jin Yanda aka canja maganar. Babak'arami ya kalleni yace, “Munubiya ce ko Munaya?” (dan basa ganemu saboda tsananin kamata da hassana ta). Zuciyata cikeda bak'in ciki nace, “Baba Munaya ce”. “yauwa Munaya, ina 'yar uwarki?”. “Tana ciki baba”. Baba ya kalli Safara'u daketa matse kwallan munafurci tun d'azun yace, “k! Safara'u tashi kiramin Munubiya ”. Batareda ta amsaba tatashi tafita, mintuna kad'an saigata sun dawo tareda Munubiya datasha kuka idanu sukayi luhu-luhu. tsaki naja a raina ina hararta ta gefen ido, rashin jarumtar ta na bani haushi, ta cika hak'uri da sanyin hali tamkar innarmu....... Maganar baba ce tadawo dani daga tunanin dana tafi. nad'ago ina kallonsa saboda kiran sunana dayayi, muryar a dake na amsa da “na'am baba”. kallonsa ya maida kan Safara'u yana fad'in “wacece acikinsu kika gani tareda Saddik'un?”. Binmu da kallo Safara'u tayi, cikin matse kwalla tace, “baba niba ganesu nakeba, sai sun banbanta min Kansu sannan”. Baice komaiba dan shima yasan da hakan, (ta hallaya ne kawai kowa ke banbantamu agidan, hatta da innarmu kuwa). Baba yabimu da kallo alamar son sanin wacece acikinmu. Da sauri Munubiya tace, “baba nice”. Nima na kar6e da fad'in “baba k'arya takeyi nice jiya Sadeeq ya aiko kira, kuma babu wata alak'a dake tsakaninmu, hasalima ya kirani ne akan Safara'un, sune dai suka maida zancen haka”. Daga Safara'u har mamanta harara suka ballamin, babu ragi nima na rama kuwa. Baba ne yakatsemu da fad'in “miya faru to Munaya?”. Janye idona nayi daga Kansu na maida gareshi, kaina ak'asa Nace, “baba ya kirani ne yana tambayata minene abinda Safara'u tafiso a rayuwarta, dan yanason yabata gift na birthday d'inta, kuma soyake yayi mata bazata. shinefa nake lissafa masa muna dariya saboda ina cewa ya had'o mata da gyad'a soyayya dan ita mayyarta ce, a dai-dai lokacinne kuma na hangota zata shigo gida, nifa dama tsokana namata gwalon, Ashe ita ta d'aukeshi wani Abu. Kuma wlhy Rahma k'arya takeyi, lokacin data fito tareda yaa Hameed ta ganni yana bani kayansa nakai masa ciki shi zai shiga masallaci salla. Wannan shinefa abinda yafaru, shine suke cewa nakwace mata Sadeeq, har ana cin zarafin innarmu da farar safiyar nan”. Ajiyar zuciya innarmu ta sauke a hankali, taji dad'i daba abinda suke zargin baneba. Wata uwar harara baba jafaru ya watsama maman Safara'u, “kai Suwaiba kedai ALLAH ya gyaraki, dan ALLAH kuringa bincike akan Abu idan yara sun fad'a muku, tokinji dai abinda yafaru, kekuma Safara'u dayake bakida tarbiyya har bakinki yana iyama Ai'sha rashin kunya ko, ki tabbatar saina saka Abdulhameed yacimin ubanku keda Rahama yau a gidannan. Ai'sha kiyi hak'uri dan ALLAH ”. Innarmu ta yink'ura zata mik'e tana fad'in babu komai babansu, ALLAH ya kauda fitinar gaba”. “Amin” muka fad'a muma muna mik'ewa mukabi innarmu a baya. Koda muka fito, sai matan gidan suka zubo mana ido suna kallo tamkar yau suka fara ganinmu, a raina nace munafukai, haka zaku k'are. Ran innarmu ya6aci matuk'a a wannan karon, amma kasancewarta mutum mai hak'uri da shanye damuwa sai bata nunaba. Nida Munubiya kam kasa shanye 6acin ranmu mukayi, munsan koma wace irin wulak'antawa za ai mana agidan *KAKARMU* ce taja mana, itace tabada kowacce iriyar k'ofar tozartamu, idan kaga abubuwan da ake mana saika d'auka ba jinin gidan baneba, tunda muka taso a haka muka tsinci kanmu, hakama mahaifiyarmu a wannan halin muka risketa tana fuskantar k'ask'anci da wulak'anci daga Kakarmu da matan Abban mu, harma da matan k'annensa, bamuda 'yanci irin na 'ya'ya, mahaifiyarmu batada kima irinta matar gida (Uwargida), hakan yasamo asaline dalilin................✍🏼 👎🏻 Tofa masu karatu dalilin mi? Dani daku duk muna buk'atar jin wannan dalili a bakin MUNAYA!, saiku kasance dani danjin Yanda wannan labari mai d'unbin harmutsi da tsalle-tsalle zai kaya, miye manufarsa? ina kuma ya dosa?. Amsa d'aya zan iya baku.👇🏻 *_LABARIN MAI TSAWONE_* saikun kasance dani a hankali zancigaba da warware muku lauje cikin nad'i. ALLAH yasa zaku bani had'in kai, tabbatarwata shine yanda zaku kar6i wannan labarin. Dan haka kumuje zuwa🥺✍🏼✍🏼 Zamu cigaba Monday insha ALLAH, wannan d'and'anone. Sannan wannan karon zandinga typing ne Monday to Friday kawai insha ALLAH, kunga banda weekend kenan😊. One luv🥰 *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu😭👏🏻._* [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _Ban yarda wani yaymin amfani da labarin nanba tako wace irin hanya, idan hakan tafaru ban yafeba gsky, ALLAH yabani ikon fad'ar abinda zai amfanar dani da Ku, ya tsare harshena daga fad'ar abinda zai cutar damu baki d'aya._ *_ALLAH ka gafartama mahaifina da dukkan sauran musulmai dasuka kwanta dama, kabama marasa lafiyarmu lafiya👏🏻._* 👉🏻2⃣ ...........Zan iya ce muku fitinar gidanmu ta farone daga tushe, dan kuwa ginannen abune tun zamanin k'uruciyar iyayenmu... Malam Faruku shine kakanmu, matarsa d'aya Marwa'natu (Innaro), 'ya'ya hud'u suka Haifa a duniya, maza uku mace 1. Auwal, Hameesu, Saffiya, Jafaru. ALLAH yayi Innaro mace mai mugun son abin duniya, arayuwarta tanason ace komai daga gareta aka fara ganinsa, kokuma wajen 'ya'yanta, sun tsayama 'ya'yansu duk sunyi karatun addini dana boko, sai dai Safiya iyakarta primary aka mata aure. Sukuma mazan duk sunkai matakin babar makaranta (jami'a). wannan yasaka Innaro d'aukar burin duniya ta d'ora akan 'ya'yan, harma matan dazasu aura. Auwal shine yafara kammala karatunsa, dan haka Malam faruku mahaifinsu yace ya fiddo matar Aure. Bai wani tsaya Jan rai ba ya gabatar da Ai'sha amatsayin wadda yakeso. Kai tsaye innaro tace sam bata aminceba, d'anta bazai auri d'iyar buzayeba kuma 'Yar iska, Auwal yayi lallashin yayi rok'on akan fahimtar da ita sonda sukema juna shi da Ai'sha, amma Sam tak'i saurarensa balle ta fahimcesa. Da farko Malam faruku yasaka musu ido, azatonsa innaro zata sakko cikin sauk'i, amma ganin yanda ta kafe akan bakanta saiya sanya baki da tambayarta dalilin k'in amincewar. Kai tsaye tace batason su Ai'shar ne, Dan ba'asan asalin suba, sannan kuma 'Yar iskace, shima kuma yasani ai. cikin hikima Malam yaso fahimtar da ita halin k'addara kowa da irin tasa, itama Aishar bayin kanta bane ba, amma tak'i saurarensa shima. ganin abin zai tasamma rashin mutumci yace to aure tsakanin Auwalu da Ai'sha kamar anyi an gama. A wannan lokacin ba k'aramin birkicewa innaro tayi musuba, amma Malam faruku yace tayi tagama, dan hujjarta batada muhimmancin dazai haramta auren Auwal da Ai'sha. babu 6ata lokaci kuma aka fara shirin bikin. *Wacece Ai'sha?* Ai'sha d'iyace gawasu buzaye 'yan k'asar Niger wad'anda k'addarar rayuwa ta jawosu zuwa k'asar Nigeria, su biyu kacal iyayensu suka Haifa, Aisha itace babba, sai k'anwarta Rabi'atu, wurjanjan suka shigo k'asar Nigeria, sun fara rayuwane awata tashar mota, inda anan tsautsayi ya fad'ama Ai'sha wani mara imani yamata fyad'e anan cikin tasha da daddare, randa abin yafaru Malam faruku yaje tashar zai bada sak'o akaima wani d'an uwansa dake garin Maiduguri, ya taras anata cecekuce atashar, yayinda Ai'sha da iyayenta ke rungume da d'iyarsu sunata kuka da kururuwa. Malam faruku yatambayi abinda ke faruwa daga wajen mutanen dasuka zagayesu suna kallo, babu 6ata lokaci matashin saurayi yafad'a masa komai. Hankalin Malam faruku yayi matuk'ar tashi, danshi mutumne mai kishin al'umma, anan ya d'auki Ai'sha da iyayenta suka nufi asibiti, saboda jinin daketa zuba daga jikinta (Dan bazata wuce 15 ba sannan), duk wata kulawar da yakamata anbama Ai'sha a asibitin, har tsawon kwanaki hud'u tasamu lafiya sarai, kamarma komai bai faruba, sai dai tabo Na zuciya da aka bar mata itada iyayenta. tun suna zaman asibiti Malam faruku ya fiskanci iyayen Aisha basuda wajen zama, dan haka yak'udiri niyyar taimakonsu. Akwai wani d'aki k'arami ciki da falo dake gidansa, saiya zagaye musu shi da Katanga yamasa gyara. Tunda aka fara aikin innaro ta tada hankalinta, duk zatonta aure zai k'ara, ganin tana neman tara masa k'asa ya zaunar da ita yamata bayani dallah-dallah, maimakon ta kwantar da hankalinta tunda ba kishiyar bace saima takuma tadashi, tace bazata zauna da iyayen Aisha ba. Malam faruku yace bata isaba, Dan gidansane babu mai hanashi ajiye Wanda yakeso akuma lokacin dayaso. Dole badan innaro tasoba su maman Aisha suka zauna agidan, sai dai ko kad'an basajin dad'in zama da ita, kullum gori da cin mutunci take musu, su Aisha kam basuda sakat awajenta, saita koma sakasu aiki tamkar boyi-boyinta. Malam faruku ne ya koyama mahaifin su Aisha sana'a, har shima yasamu rufin asirin rik'e iyalensa dai-dai gwargwado, amma ko kama k'afar Malam faruku baiyiba, lokuta da fama ma shine ke taimakonsa dawasu abubuwan Na rayuwa, musamman d'inkin sitturar su Aisha da wasu matsaloli Na yau da kullum dasukan taso. tun zuwansu gidan Auwal yafara k'aunar Aisha, duk da mahaifinsu ya Sanar musu da komai akan k'addarar da ta fad'ama Aishan kuwa, shekararsu biyu suna soyayya, tun Aisha Na d'ari-d'ari dashi saboda tsoron abinda aka aikata mata har tazo tasaki jikinta dashi, sai dai babu Wanda yasan suna soyayyar sai Rabi'a k'anwarta. Ana haka kuma Auwal yazo da zancen Aisha zai aura. To haka dai akayi auren Auwal da Aisha badan innaro tasoba. Wannan kuma yasakata d'aukar Karen tsana ta d'orama Aisha, kullum cikin zagi da cin mutuncin Aisha take, sosai tazamar mata Uwar miji mai kishi da sarakuwa, ga gorin datake mata akan ita 'Yar iskace, babu wani fyad'e da'aka mata, taje tayi iskancinta an fake da fyad'e an dawo an lik'ema d'anta da asiri, tujara dai iri-iri dai ta innaro. Aisha tanada hak'uri, ko kad'an abinda innaro kemata bai hanata girmamata ba da bata matsayi irinna uwa, amma innaro bata gani. Watan aurensu 7 kacal innaro ta samoma Auwal wata yarinya mai suna Mero, mero d'iyace ga wani matashin d'an kasuwa, tun alokacinma ana lissafashi a masu kud'in yankin balle yanzu daya zama shahararre, Auwal bayason Mairo, amma dolensa ya aura saboda innaro tace zata tsine masa. Shigowar Mairo Yakuma k'untata Aisha a gidan, dan tunkan ta shigo innaro tagama 6ata sunan Aisha dana iyayenta awajensu mairo, shigowar mairo da wata 1 kacal kuma tasamu ciki, wannan fa yakuma k'ara ta6ar6arewar al'amura, gashi sannan ALLAH ya yalwatama Auwal d'in babu laifi, harma yasayi wasu filaye uku shida 'yan uwansa anan cikin anguwar kusada su innaro, amma ba'a ginaba, dan babu kud'in ginin lokacin. A wannan lokacinne kuma k'addara ta afkama iyayen Aisha, ranar wata alhamis da daddare aka maka ruwa Na tashin hankali, Wanda yay sanadin fad'awar d'akin dasuke ciki suka rasu. Aisha da Rabi'a sunshiga matuk'ar tashin hankali, hakama Malam faruku, innaro kam ko'a jikinta. Rasuwar iyayen Aisha yasaka rabi'a k'anwarta dawowa hannunta da zama, akuma lokacinne Hameesu shima yace Rabi'a yakeso da aure. tashin farko innaro ta taka masa birki da kukarin zata tsine masa kuwa. dole yabar maganar auren Rabi'ar yasamo wata Ruk'ayya ya aura. A lokacinne Mairo ta haihu namiji, zokaga murna wajen innaro da mairo, Malam ma yayi murna, hakama Aisha, dukda innaro tace Na munafurcine. ranar suna yaro yaci Abdulhameed, koda wasa mairo bata ta6a yarda Aisha ta d'auki hameed ba, dan innaro tahana, Auwal yayi fad'an shida Malam harsun gaji. Rayuwa tacigaba da tafiya tsawon shekaru, zuwa sannan su Auwal sun had'a hannu sun gina filinsu, kowa da 6angarensa, gidanmu yafara yawaita da 'ya'ya, dan matar Hameesu ma ta haihu Namiji Shafi'u, hakama matan gidanmu sun k'aru, dan jafaru ma yayi aure, hakama Hameesu yak'ara aure shima, ga iyayenmu sun kuma bunk'asa, dansu wuce buk'atun yau da gobe, dai-dai gwargwado akwai rufin asiri agaresu, alokacin kuma sai Auwal yakuma auro ta uku, auren iyayenmu yakoma tamkar gasa wajen za6o 'ya'yan manya, dan kuwa Aisha ce kawai d'iyan talakawa acikinsu, tana zaunene kawai da k'arfin ALLAH dakuma Na Malam faruku, saikuma soyayyar mijinta Auwal, amma da dan ta innaro ne da tuni Auwal ya saketa. Akwaima randa fada ya had'a mairo da Aisha akan Rabi'a ta doki hameed saboda yamata rashin kunya, dukan da mairo taima Rabi'a saiya sa Aisha kasa hak'uri a ranar ta tanka mata, nankuwa mairo tafara zuba mata gori da cin zarafi, da innaro tazo danjin ba'asin rigimar saitace dole Auwal yasaki Aisha, dukda kuma mairo ce mai laifi, Auwal yayta magiya amma innaro tace yaza6a ko ita ko Aishan, babu yanda zaiyi yasaki Aisha saki d'aya alokacin. Hankalin Aisha yatashi matuk'a, dan batasan inda zasu dosaba, tunda basuda kowa a Nigeria, ga innaro tsaye akanta tace atake saita bar mata gidan d'a. ALLAH ya tak'aita abunne dai-dai sanda Aisha ke fitowa rik'eda hannun Rabi'a kuma saiga Malam faruku yadawo daga kasuwa, nanfa ya tambayi ba'asi, Aisha tasanar masa komai, maidata yayi gidan, yakuma saka Auwal ya maida aurensu atake awajen, sannan ya tabbatar masa ko bayan babu ransa yasake sakin Aysha bai yafeba, kuma inhar innaro tasake sakashi ya saketa itama abakin aurenta. Wannan shine dalilin dayasa auren Aisha da Auwal bai sake rawaba. rayuwa kuma tacigaba da shurawa. Matan gidanmu 7. Auwal matansa uku, Aisha (innarmu) Mairo (mama) Sadiya (gwaggon haleema) Hameesu nada biyu, Ruk'ayya (umma) Hadiza (momy) Jafaru Nada biyu shima, Suwaiba (maman safara'u) Hafsatu (maman Fauziyya). Kowacce ta haihu acikinsu, amma banda Aisha, wadda saida sukayi shekara 20 da aure itada Auwal sannan ALLAH yabata ciki, zokiga murna wajen Auwal da ahalinsa, saidai banda matan gidanmu da innaro, dan aganinsu duk sunfi Aisha matsayi, (maman fauziyya) Ce kawai babu ruwanta, dan suna d'asawa da Aisha sosai, ita kad'aice bata raina innarmu ba, dan Yaya ma take cemata. Babu irin wahalar da Aisha batasha agidanba acikin shekarunan, kullum cikin mata gorin haihuwa dana talauci ake, harma dana batada asali, tundaga kishiyoyinta har matan k'annen mijinta basu raga mataba, kowacce jitake ina wuta tasaka innarmu a gidan, dama ga d'aurin gidi daga innaro suna samu. innarmu bata cemusu komai, saidai tashiga d'aki tasha kukanta, 'ya'yan maman fauziyya ne kad'ai ke shigowa d'akinta, amma sauran duk an hanasu, gashi ta aurar da Rabi'a tuni, itama harta haihu uku ma. to saikuma ga Aisha da ciki rana tsaka, bayan tagama fidda ran haihuwarma gaba d'ayanta. cikin ikon ALLAH cikinta yakai haihuwa, ranar data haihu saiga 'yan biyu k'yawawa kamarta duk mata, A zahiri matan gidanmu suna k'untatama innarmu ne saboda yanda innaro tagama 6ata Aisha awajensu, a bad'ini kuma suna k'in Aishane saboda tafisu k'yau da komaima Na halittar jiki, (dan cikakkiyar buzuwa Ce) mai k'yawu Na asali, dirarriyar macece doguwa, fara tas, gashin kai, idanu da komai ALLAH yabatasu. Sa6anin su daba haka sukeba. cikin ikon ALLAH kuma saigashi ta haifo 'ya'yanta masu tsananin kama da ita. Hassana (Munubiya) da Hussaina (Munaya) wad'anda suke matuk'ar kama da juna, kamar Munaya da Munubiya ta 6aci matuk'a, ko Aisha saitayi da gaske take banbancesu, saida suka fara girmanema ake d'an banbantasu tawajen halayya shima ba kowaba, amma Aisha ita tana ganesu kai tsaye a sanan. Munubiya tanada hak'uri tamkar Aisha, duk wahalar dasukesha wajen yaran gidan bata iya ramawa, saidai tasha kukanta tashare hawaye. sa6anin Munaya da take fitinanniya, bata bari a cuceta, koda anfi k'arfinta saitabi tawata hanyar tarama kuwa, wannan yasaka matan gidan da yara sukafi tsanarta, sai dai kuma basa iya banbancesu itada Munubiya, sometimes Munaya takanyi laifi akama Munubiya a daka, itakuma Munubiya bazata ta6a fad'in ba itaceba. Ganin hakan yasaka Aisha yima Munubiya shaida saboda aringa banbantasu, amma Munaya Na k'yalla ido tagani sai itama tayima kanta irin ta Munubiya komai da komai, idan sau dubu akama Munubiya shaida ajiki Munaya ma zataje taima kanta, hakama Munubiya takanyi idan anyima munaya, hakan yasa Aisha ta hak'ura kawai harma suka Shiga makaranta, nanma rikicin Munaya bai k'areba, dan saima abinda yay gaba, tajawo fad'a akama Munubiya adaka, hakan kuma bazaisa gobe ta fasaba. Shekarar su goma Aisha takuma haihuwar 'yan biyu duk maza, Aryaan da Aiyyaan, tundaga lokacin kuma bata sakeba. Sai dai Munaya da Munubiya suna matuk'ar k'aunar junansu over abinma har saiya Baka mamaki, sannan suna k'aunar mahaifiyarsu da k'annensu, Munaya ce kan shiga idan ana cin zarafin mamansu, amma ita Munubiya saidai taita kuka. Yanzu haka zancen danake muku shekarunmu 19 nida Munubiya, muna matakin farko a jami'a, munzama 'yan mata, k'yawunmu da tsananin kamarmu da innarmu yasake fitowa, mun fita daban a gidanmu, dan mukad'aine kamarmu daban, Ayyan da Aryan ma duk Abbanmu suka kwaso, wannan yasaka suke kama da 'yan gidanmu. Tabbas bamajin dad'in zaman gidanmu, saboda k'unci da hantara damuke fuskanta muda mahaifiyarmu awajen Innaro da matan gidan, harma dawasu yaran gidan 'yan uwanmu, amma wasu muna shiri dasu sosai, musamman ma mazan yayyenmu manya, dansu babu ruwansu da gutsiri tsomar cikin gidan. Gidanmu gidane tamkar gidan hayar daya had'a k'abilu daban-daban saboda yawan rikici, kullum cikin fad'a muke, ba iyayenba ba yaranba, kai kace muna ganin hanjin junane. Gwargwadon iko akwai hali a gidanmu, dan iyayenmu sun rik'e gidanmu sosai da buk'atinmu, dukda yawa da ALLAH yabamu, bamu rasa ci da sha ba da situra, hakama matsalolin karatunmu, dan kai tsaye zance gidanmu gidan 'yan bokone, kullum cikin gasa da juna ake, burin kowa ace shine gaba, batun ilimin addinima kam Alhmdllh, dan tsaye iyayenmu suke akanmu, har gobe yaa hameed bai daina zama gaban malamai ba balle mu 'yan baya-baya. ak'alla yaran gidanmu munkai mu 43 kuma. ALLAH yayma Malam jafaru kakanmu rasuwa shekara biyu kenan, innaro Ce dai tana nan daram, al'amuranta sai abinda yay gaba, dan har gobe bata k'aunar innarmu, kuma bata daina cin zarafinta ba agaban kowa da mata gorin rashin dangi. Hakan yasa kullum cikin buri da k'udirin binciko dangin Innarmu nake, ko itama zata samu 'yancin kanta kamar kowa😢. Wannan shine labarin gidanmu, sai ahankali zaku cigaba da fuskantar ainahin halayen jama'ar gidanmu da aiyukansu, harma da sunayensu😊.............✍🏼 To masu karatu, sai nace yanzufa za'a fara, saiku kasance dani danjin labarin *_RAINA KAMA.... kaga gayya_* dan akwai babban al'amari a gaba, bawai gidan su Munaya kawai labarin ya shafaba, akwai wani lauje cikin Nad'i daga d'ayan 6angaren labarin Na Raina kama.....😉 suga gayya ba👎🏻😄. One luv🥰 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu😭👏🏻_* [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻3⃣ .........Fad'a sosai innarmu tamin akan Marin Safara'u danayi, sannan ta d'ora da nasiha kamar yanda tasaba, wani kam yashiga kunnena, wani kuwa tabaya yabi, dan harga ALLAH Na daina zama kowa yana taka mana mahaifiya a gidan. Innarmu tace, “ku shirya gobe idan ALLAH ya kaimu Ku tafi gidan mamanku Rabi'a Ku k'arasa hutunku, banason zamanku a gidan nan tunda fitina yake kawowa”. A sanyaye Munubiya ta amsa da “to innarmu”. Amma ni saina tunzuro baki gaba ina k'unk'uni, dan banason tafiya ko ina, canma saboda d'an mama Rabi'a d'inne Marwan, ko kad'an bama shiri dashi, saboda masifarsa. “kai innarmu, yanzu dan ALLAH saboda wasu can bazamu mik'e kafa yanda mukeso ba agidanmu, duka fa hutun sati biyu ne kacal, amma saimunje wani waje?, ni wlhy inkika barni babu mai k'ara mana koda kallon banza a gidannan, harma innaro bazan bartaba.........” Maficin danaga innarmu tajawo yasani tashi da sauri nabar gurin, Na tabbata shirin bugamin takeyi. Munubiya ta saka dariya tana kallona, “ke ga rashin arzik'i ga tsoron tsiya, dukan maficin kikema wannan gudun?”. Harara Na balla mata, “yo k'ya fad'i haka mana tunda ba jikinki baneba, tsoro kam kinsan waye matsoraci acikinmu ai”. Munubiya ta ta6e baki “naji dai, koma mizaki ce kije kiyita cewa, inama kayana dakika saka jiya? na wanke, dan dasu zanje”. Wayar innarmu Na d'auka ina dannawa, batareda na bata amsaba Na nuna mata laundry basket d'inmu. Innarmu tace, “to Aljanar waya ajiyemin kafin ki k'ararmin kud'in ciki, ina taki?”. “kai innarmu, please mana, zan kira Ayusher nefa nasanar mata muna zuwa gobe, ALLAH wayata babu ko nera aciki Munu ta cinye min jiya”. “kiji tsoron ALLAH munaya, Nina cinye mini kud'in waya? bake kika kira Balkisu ba da kanki?”. “to dana kirata sai nace kuyita surutu har kud'ina ya k'are” innarmu Na shirin yin magana muka jiyo kururuwar kukan Safara'u da Rahama. dariya Na k'yalk'yale da ita, ina fad'in “o, ALLAH ga yaa hameed can yana gwajin kwanji a jikin gayu”. Harara innarmu ta ballamin, saikuma tamik'e tana shirin fita, nasan kar6arsu zataje, nai saurin fad'in “kai innarmu, kid'an barsu su lallasu mana”. Dakk'uwa ta watsomin tareda fad'in “K'aniyarki Munaya”. Dagani har Munubiya dariya muka sanya harda tafawa kuwa. Ba'a rufa mintuna 3 da fitar innarmu ba muka fara jiyo hargowar Maman safara'u (dama ita bata magana a hankali) Yaa hameed takema masifa akan dukansu safara'u dayakeyi, maman su yaa hameed babu hak'uri, itama tafito suka fara cacar baki, yaa hameed kam ficewarsa yayi bayan innarmu ta kwaci su Rahama a hannunsa da k'yar. kafin kace mi gidan yakuma kaurewa. Munubiya tace, “kai jama'a ko breakfast ba'ayi agidanba har antafi wrestling zagaye na biyu”. Na fad'a saman gado ina Dariya, danni mamaki 'yan gidanmu nakeyi da bala'insu. wayar Innarmu tayi ringing, da Sauri Na duba sainaga Abbanmu ne, cikeda d'oki Na amsa tareda masa sallama sannan Na gaidashi. Yace, “Munubiya ina maman takune?”. “Abba ba munu bace, nicefa”. “to to munaya ce? hayaniyar mi nakeji haka agidanne Munaya?”. K'yafta min ido da zungurina Munubiya tashiga yi wai karna fad'a masa (dayake a Hans free nasaka wayar, tana jin komai) amma saina harareta da murgud'a baki nace, “Abba Mama Ce da maman safara'u suke fad'a”. Tsaki yaja da fad'in “ALLAH ya shiryesu to, ina maman taku ne?”. “Amin Abba, Innarmu tana can wajen rabon fad'an ai”. “shike Nan, idan tashigo kice takirani muyi magana”. “to Abba bye”. Yace, “ok dear bye”. Sannan ya yanke wayar. Ina yanke wayar Munubiya ta kaimin bugu, Na kauce ina dariya “yo da bakina a hanani fad'ar gaskiya”. “ba hanaki akayiba, amma kinsan idan Allura ta tono garma mune tushen fad'an ai, kinkuma san halin Abba da d'aukar zafi kamar baba k'arami”. “tab, ta k'are musu dai suda suka takalo wlhy, jarababbu dangin masifa”. “kina ciki kenan tunda kema dangin kine ai”. Dariya muka Sanya nida munubiya. *washe gari* Tafiyar mu gidan mama Rabi bai yuwuba, saboda dawowar Abbanmu, da innarmu ta sanar masa a waya zamuje can muk'arasa Hutu sai yace a'a muyi hak'uri mu zauna, Dan akwai bak'in da zaiyi a k'arshen sati (weekend), kuma yanason dukkan yaran mukasance muna nan. Innarmu tace shikenan. Wannan dalilinne ya hanamu tafiya Hutu, dama ni ba so nakeba, Munubiya ce keta zakwad'in tafiyar. Yau ta kasance alhamis, tunda safe muka tashi da himmar wanki nida Munubiya, ina sharar sashenmu Munubiya na fidda kayan wankin, yayinda Aryan da Aiyan keta tara mana ruwa daga fanfo zuwa banbu. Ina gama sharar na wanke hannuna na k'arasa bakin fanfo inda Munubiya ke k'ok'arin jik'a kayan. zama nayi bisa d'an dakali da akayi wajen saboda irin hakan, wanki ko wanke-wanke da sauransu, waya nake latsawa ina nemo mana wak'a, dan muji dad'in wankin, maganar aunty khaleesa kawai mukji a kanmu tana fad'in, “k! Munaya tashi kije ki gyaramin d'akinmu, akwai wani zanina nan ki d'akkosa ku wankemin”. Banza namata ban d'agoba, sai Munubiya ce tace, “to aunty khaleesa”. Shirun danayi ina kuma tamke fuska yasata gane nice munaya, Dan haka ta kalli Munubiya dahar tatafi, “k Munubiya!... dawo, bakece zakiyiba, k! Dan uwarku Munaya tashi kije kimin”. Da sauri Munubiya tace, "Aunty khaleesa ai nice munaya, waccan Munubiya ce”. Hararta tayi, “mai dani 'yar iska to, ko kina tunanin ban ganeku nima d'in?”. Banyi niyyar d'agowa ba, amma jin abinda tafad'a yasani sakin guntun murmushi, nasan k'arya takeyi tace tana ganemu kai tsaye, yanzu ma dan kawai na nunu halin nawane shiyyasa tagane nice, kawai tafad'ane dai, mai da kaina nayi nacigaba da abinda nakeyi....... Wata ashar ta lailayo ta makamin, tareda zaburowa tamkar zata dakeni, dai dai nan sallamar innaro ta karad'e tsakar gidan. mu duka kallonta mukayi, nikam kallo d'aya namata na d'auke kaina, (dan nikam natsani kakarnan tamu) Munubiya da aunty khaleesa suka gaidata, nikam a d'age nace “ina kwana”. “kin yima uwarki Ai'sha dan Ubanki”, cewar innaro ta na nunani da d'anyatsanta manuniya👉🏻, tacigaba da fad'in “ni zakima gaisuwa a haka? kamar wata sa'ar uwarki?, aiko Aisha da ubanki basu isa sumin gaisuwa hakaba balle ke haihuwar yanzun”. Baki na la6e, ba tareda na kalleta ba natashi nahau wankin, Munubiya kuma tawuce danta gyarama su aunty khaleesa d'akinsu. abinda nayi na nuna halin ko in kula saiya kuma tunzura innaro, ta fara hayagaga da matse kwalla wai naci zarafinta. Wannan yasaka matan gidanmu da yara fara fitowa d'ai-d'ai suna kallonmu (dan al'adar gidanmu ce hakan, da anji kaya-kaya kowa zaiyo waje yaganema idonsa abinda ke faruwa). Dady ya k'araso da sauri yana fad'in “Inna miya farune haka da kuka? Keda waye?”. “wannan shed'aniyar yarinyar mana” tayi maganar tana nunani “waini yarinyar nan zataima d'ibar albarka saboda uwarsu kullum tana aibantani a gurinsu, shiyyasa duk sun rainani....” Baki bud'e nake kallon innaro da sherinta. wlhy wannan tsohuwar bazataga Annabi ba........ Maganar Dady ta dawo dani daga mamakin innaro. Yace, “Munaya ce ko Munubiya? miya farune keda inna?”. Dady yanada sauk'i, ba kamar Abbanmu da baba k'arami ba sun fishi zafi. Nace, “dady Munaya ce. wlhy babu abinda namata, kawaifa daga shigowarta duk muka gaidata, shine kawai ta hau zagina wai ban gaidata da k'yauba.......” “amma ai gaisuwar rashin tarbiya kikai mata”. ‘cewar Aunty khaleesa’. Dady zaiyi magana Aunty Ramlah tace, “wlhy Dady ba haka bane, duk abinda yafaru akan idona yafaru, dan nafito zan d'iba ruwa a fanfo”. Dakuwa Innaro ta mata, “kinci uwarki hadiza, kema ashe munafukace ban saniba, to ko hadizar ta haifama Ai'sha ne ke?”. Fakar idon Dady aunty Ramlah tayi ta dallama innaro harara, sannan tace, “yo daga fad'ar gaskiya, nidai wlhy Dady abinda nagani nakuma ji kenan”. Girgiza kai Dady yayi, sannan yace, “kiyi hak'uri Inna, Munaya tayi kuskure amma bazata sakeba. Munaya zoki bata hak'uri”. Ban musaba nazo har gabanta nace tayi hak'uri, bata amsamin ba, saima hararata datayi kawai. nima saina bar wajen nakoma kan wankina. Dady Yakama hannun innaro suka shiga falonsa, matan gidanmu duk suka bar wajen, basuso wasan yak'are a nanba, sunso ace cin mutuncin innaro yasauka har kan innarmu. Innarmu dake tsaye daga k'ofar falonta tanajiyo abinda ke faruwa dukda katanga ta shiga tsakiya, ta girgiza kai kawai tana komawa ciki da fad'in ALLAH ya k'yauta. Ina wanki ina zubda hawaye, sosai raina ya sosu yau akan abinda Innaro tamin, dukda bawai yaune karon farko da hakan ya faruba, sai dai na yau yamin zafi ainun, har inaji natsani zaman gidanmu, a fili na furta ALLAH kabamu miji muyi aurenmu mubar gidannan”. Munubiya dabansan tazo wajenba naji ta amsa da Amin sweetheart, wlhy koni yanzu addu'ar danake mana kenan, sai dai banason mutafi mubar innarmu a wannan halin dasu Aryaan”. “hakane Munu..., karki damu, insha ALLAH munayin aure d'auke innarmu zamuyi ko Abbah ya yarda kobai yardaba wlhy!!”. ‘ta k'arashe maganar a harzuk'e’. Murmushi Munubiya tayi, dan tasan ran 'yar uwar tata yakai k'ololuwar 6aci. Har muka gama wankin innaro na gidan bata tafiba, bamusan uwarmi takeyiba. dayake girkin gwaggon Haleema nema ranar. ina tsaye a bayan flowers d'in d'akinmu ina goge glass d'in windows naga Abdul yafito d'aukeda tire an jera sabbin kuloli akai, nasan Abbanmu baya gari, dan haka nace, “Abdul wazaka kaima abinci haka?”. Yace, “Aunty zan kaima innaro tana falon dady”. Kai na jinjina masa kawai nace jeka, cigaba nayi da aikina ina fad'in “shidai munafurci ai dodone, maishi yakeci”. Koda na koma ciki sai nake bama Munubiya labari, innarmu dake bayanmu bamu saniba tace, “to ina ruwankine wai Munaya?, nifa banason gutsiri tsoma wlhy, wai sai yaushene zaku daina jamin fitina a gidanan ne?”. A sanyaye mukace kiyi hak'uri innarmu“. Batace komaiba tashige d'akinta, muduka da kallon tausayi muka bita, dukda tasan ita ake tauyema hak'i amma bata ta6a nuna itace mara laifi, kullum ta amince itace a k'asan kamar yanda kowa ke kallonta agidan. ★★★★★ Washe gari Abbah yadawo da yamma, duk munyi murnar ganinsa, shima kuma hakan take a garesa. Sai da daddare suka tara iyayenmu mata meeting shida Dady da baba k'arami. Abbanmu yay gyaran murya sannan yace, “dama wani abune yasaka muka taraku, maganace akan yaranmu mata, Ramlah da khaleesa da Rahaima da Hauwa'u kowa yasan sun fida mazajen aure harma an tsaida bikinsu nanda bayan salla”. Duk suka amsa da eh. “yauwa to Alhmdllh, yanzu munada sauran yara 'yan mata agidanan ak'alla su 8, kuma duk kusan Kansu d'ayane, dukda su Ramlah sun girmemusu, to wani uzirine yataso na tilas zamu had'awa auren wasunsu danasu khaleesa. shin ko akwai wad'anda a cikinsu sukeda tsayayye? domin a fiddasu?”. Da sauri maman safara'u tace, “Safara'u nadashi, dan harma yanason turo iyayensa, amma nace ta dakatar dashi sai angama na yayyensu”. “to Alhmdllhi, sai kuma wa?”. Umma Ruk'ayya ma tace, “Fiddausi tanada tsayayye itama”. “masha ALLAH, to bayansu fa?”. “mamansu yaa hameed tace, “ai inaga sukenan kam Abban Hameed”. “yanzu su 6 kenan suka rage? to dama Alhaji halliru d'an majalissar datta6ai, nasan duk kunsan abokinane shak'ik'i? to shine yanemi alfarmar nemama 'ya'yansa maza biyu auren biyu daga cikin 'ya'yana, d'aya d'ansane na cikinsa, d'aya kuma d'an yayarsane tarasu tabari yacigaba da rik'onsa. to harga ALLAH nasan yaransa sunada tarbiyya dan haka na amince, amma dukda haka saida nasake dogon bincike akan yaran saboda yaron yanzu ka haifeshine baka haifi halinsa ba, to Alhmdllh suma basuda wata matsala, dan haka mun yanke magana dashi akan suzo saisu za6a acikinsu, wannan shine dalilin dayasa muka taraku kenan”. Hummm yaufa anzo da Sabon al'amari a gidan namu, nanafa iyayenmu mata suka hau tsugunne-tsugunne, kowa burinta ace d'iyarta aka za6a, harma da iyayensu safara'u dakeda mijin a hannu, ganin sunji gidan maik'one kowacce tafara k'ok'arin gani da fatan 'yarta ta kasance acikin gidan, aiko sai shirye-shirye kowa keyi a asirce, aka fara gyara 'ya'ya. Mudai a 6angarenmu babu abinda innarmu kemana, hasalima inda taji maganar anan ta barta, komu bata sanarma ba, sai abakin Fauziyya mukejin komai. Yanda ake shirye-shiryen bak'i takowanne 6angare saika d'auka 'ya'ya. Shugaban k'asane zasuzo, ni abinma mamaki yabani dan kowanne d'aki da nasu shirin, dayake kowane d'aki akwai budurwa d'aya, mu 8ne, su shida kowanne d'aki 1 kenan, saimu mu biyu a d'akinmu, 'ya'yan abbanmu mu 4 kenan, na baba k'arami 2 na Dady 2, gashi biyu za'a za6a acikinmu amma saika d'auka mu duka za'a za6a saboda shirye-shiryen da iyayenmu keyi. Ranar Asabar (Saturday) kenan takama zasuzo, dan haka muduka 'yan Matan 8 baba k'arami yace muhad'u muyi girkin tarbarsu. Ni Munaya, Munubiya, Safara'u, Fauziyya, Haleematu, Fiddausi, Zarah, Siyama. A kitchen d'in 6angarenmu muke girkin, dukda dai iyayenmu sun d'an saka mana hannu wajen tsara kalolin abincin daya dace a tanada. Ni abunma haushi yabani, yanda naga 'yan uwana NATA rawar kai, sai wani k'alk'ale-k'alk'ale akema abinci da drinks na gargajiya damuka had'a. A raina nace Kodai sune iyayen cin tsiya, ai bazasuci ko quarter d'in abincinnan ba, wannanma ai almabazzaranci ne wlhy, mutun biyu kawai amma anmusu abinci wajen kala 6, banda kuma kayan ciye-ciye irinsu snakes da nau'in nama da aka sarrafa zuwa daban-daban. haka dai muka gama aka kai falon baba k'arami aka shirya, sannan kowa takoma 6angarensu danta kimtsa........✍🏼 Anan ne za'ayi kece rainin👌🏻😄🏃🏻‍♀ Guys kumuje zuwa😉👎🏻 One luv🥰🥰 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*👏🏻😭 [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻4⃣ .......Daga ni har Munubiya babu wata kwalliya damukayi, hasalima ni ko mai k'in shafawa nayi, danayo wankanma sainayi kwanciyata na hau barci. sai wajen 1 munubiya ta tadani wai sun iso, dama lokacin duk fashin salla muke nida munu.... (zakusha mamaki idan nace muku dai-dai da prioud yakanzo mana rana d'aya nida hassana ta, kuma musami tsarki tare), tashinai ina yatsine fuska, dan naji haushin tadanin datayi, toilet nashiga domin kimtsa jikina, sama-sama nadinga jiyo maganar Ikram tana fad'in “Aunty wai innaro tace kuzo”. Cikeda mamaki munubiya ta amsa da to. nima abin yabani mamaki, dan haka nafito da Sauri, “wai Munubiya minake jiyowa ina toilet? ”. Maganarta d'auke da mamaki tace, “wai innaro ke kiranmu”. “ni da ke? kokuma mu duka?”. “wlhy ban saniba munaya, sai dai munje d'in magani”. Innarmu tashigo d'akin tana cewa “waishin Baku naji innaro ta aiko kira bane?”. Muka amsa da “eh innarmu, mune”. “to mi kuke jira, kuwuce kutafi mana”. Babu Wanda yay magana acikinmu muka fita muna mamakin wannan kira Na innaro. Tun a k'ofar falon baba k'arami mukaga wasu k'yawawan takalma, ga wani k'amshi yacika wajen, wicewa mukayi batareda mun shigaba, dukda mun hango Zarah da Siyama da Fiddausi natahowa cikin matsanancin gayu, saika rantse fita zasuyi wani gagarumin biki. A k'ofar gidama munci karo da motoci uku duk bak'ak'e wulik, sai dai ta tsakiyar tafi k'yau da d'aukar hankali, garadan samarine majiya k'arfi kusan su 7 tsaitsaye ajikin motocin, duk suna sanye da bak'ak'en suit, daka gansu kasan babu sauk'i, hakan yasa muka fahimci bodyguards d'in bak'inne. Gida biyu ne tsakanin gidan innaro da gidanmu, dan haka muka Isa da wuri. a tsakar gida muka isketa tana shanyar lawashin albasa. muka gaidata. Yanda ta saba haka ta amsa mana, amma tace mushiga ciki tana zuwa. Kusan mintuna 40 muna falon innaro zaune, amma bata shigoba, hakan yasakani tunanin tabas akwai wani lauje cikin nad'i a kiran namu, tashi nayi nalek'a tsakar gidan ta window, amma bata nan. “Munubiya kinsan Innaro bata gidanan kuwa?”. Cikeda mamaki tad'ago tana kallona, “kamarya bata nan?”. “Munu... Wlhy ko rantsuwa nayi babu kaffara aciki, akwai dalilin kawomu nan”. A sanyaye Munubiya tace, “karki damu Sweetheart, ko mai suke nufi ALLAH ya fisu, dama naga mamansu ya hameed tafito d'azu bayan mungama girki, ai d'an hakkin daka raina shike tsolema ido, *_RAINA KAMA KAGA GAYYAFA_* inji masu iya magana. Hakane dear. Daga nan muka zauna shiru kowa da abinda take tunani, har barci ya sace Munubiya, nukuma nahau chart kawai. A gidanmu kuwa su Siyama ne suka fara Isa falon, tundaga k'ofar falon daddad'an k'amshin turaren bak'in yafara rikitasu, sun shiga da sallama, yayinda sukuma bak'in suka amsa. Gaskiya masha ALLAH dan kuwa matasan samarine k'yawawa masu aji da gayu, suna kama da juna, hakan zai tabbatar maka da cewa jininsu d'aya. sunci ado cikin wasu rantsatstsun shaddoji gizna, sai maik'o sukeyi, d'aya yafi d'aya sakin fuska. Su Siyama sun gaidasu cikin shauk'i da zumud'in fatan kowaccensu ta kasance abar za6i. Sun amsa musu cikeda jan aji da nazartar su, ahaka Fauziyya da Safara'u da Haleematu suka shigo suma, suma dai gaidasun sukayi. Fauziyya da Zarah ne kawai sukayi hankalin tashi su zuba musu ruwa da lemo, sannan suka musu bismillar abinci. Mai d'an yawan fara'ar ne yamusu godiya, sannan yace, “to ya sunan k'annen namune?”. Cikeda yanga kowacce tafara gabatar da kanta agaresu, yayinda sukuma suka maida hankali sosai wajen nazartarsu, bayan sun gama suma suka gabatar musu da kansun. “Ni sunan Sulaiman, brother d'ina kuma Sa'eed, munji dad'i kwarai da gaske Na tarbar damuka samu daga gareku”. Murmushi duk sukayi suna nuna farin cikinsu suma, sund'an ta6a hira. Babu Wanda yadamu da rashin ganinmu acikinsu sai Fauziyya, iyayenmu kuma basusan babumu ba, dansu suna falon Abbanmu suna hira. Kusan awa d'aya sannan duk suka fito suka barsu dan sud'anci abinci. Suna fita Sa'eed ya kalli Sulaiman a yatsine, “my man nida yaran nan nakula sunada rawar kai, garama mai farin kayannan naga kamar tafisu nutsuwa (Fauziyya)”. “wlhy gskyarka bro... Amma Kasan dolenefa mucika umarnin dad, tunda yayi rantsuwa akan dolene muza6a acikinsu, kai wlhy mun jama kanmu, ni dama tun maganar farko da dad yamana Na maida hankali naza6o da duk hakan bata faruba gareni”. Cikin ta6e baki Sa'eed yace, “wannan kuma kaika Sani malam. amma basuma 8 akace manaba?”. “eh hakane, amma kamanta ance biyu acikinsu sunada samari”. A nanma bakin Sa'eed Yakuma ta6ewa. sun d'anci abinda aka ajiye musu, sannan su Abba suka shigo suka gaisa, cikeda girmamawa suka gaida su Abba, hakan yayima Dady da baba k'arami dad'i, sun kuma tabbatarwa yaran sunada tarbiyya, dama basa kokwanto akan zance yayan Nasu. An musu rakkiya duka Sassan gidanmu, sun Haida iyayenmu mata. ganinsu Yakuma rud'ar da iyayenmu, kowacce addau'arta ALLAH yasa d'iyarta aka za6a, yo wad'annan zuk'a-zuk'an samari haka, ga kud'i ga ilimi, kowacce saida suka ajiye mata kud'i suke fitowa, har innarmu ma. Tun aiko kiranmu Innarmu taji ajikinta da biyu aka turamu can, amma baiwar ALLAH hakan bai dametaba, tasan dai wata bata aurar mijin wani, dan haka ko'a fuska bata nunama wani bama cikin wad'anda suka je wajen bak'inba. Saida Innaro takusa awa d'aya sannan tashigo gidan, yinai tamkar ban gantaba, Munubiya kam tanata barcinta, itama sai bata kulaniba tashige bedroom d'inta. Shigarta baifi da mintuna 3 ba mukajiyo sallama a k'ofar d'akin, nice Na amsa, Basheer yafara shigowa, sai kuma Sulaiman da Sa'eed, irin k'amshin damukaji a k'ofar d'akin baba karami yasani d'agowa dan jinsa anan, hakan ya tabbatar min da sune sukazo gaida Innaro. Tunda suka shigo idonsu ya sauka a kanmu, sun kasa d'auke kai daga kallonmu. Cikeda jan aji nace, “ina yininku”. Duk suka amsa da “lafiya big girl”. Basheer yace, “kai Aunty dama kuna nan Ku?”. Kallonsa nayi nace, “eh, ana nemanmu ne?”. “a'a, amma dai ba'asan badaku akaje wajen bak'iba”. Hararsa nayi, saboda sanin halin shegen surutunsa, “malam kaje ka kira musu Innaro ka zauna kana zubama mutane shegen surutu uwa aku”. Baki ya zum6ura sannan yanufi bedroom d'in Innaro. Wanda tunda suka shigo yakasa d'auke kai daga kallona, saima zama dayayi kujeraf dake kallona yace, “ok dan bakwa buk'atar ganinmu kuka gudonan kenan? Sai kuma gashi ALLAH ya kawomu mun ganku, dama ance rabon kwad'o...... koko my man?”. Murmushi Sulaiman yayi, yace “hakane wlhy bro, hakanma dasukayi yamana dai-dai”. Magan ganinmu yasaka Munubiya tashi, Sulaiman yace, “sleeping beauty kin tashi?”. d'an waro idanu Munubiya tayi, sai kuma ta kalleni dan neman k'arin bayani. Innaro takatsemu da fad'in “toku kuna ganin bak'i basai Ku tashi Ku basu wajeba”. “cikin tsokana Sulaiman yace, “a'a Granny idan sun tashi wazamu kalla? Sun gudo wajenki dan karmu gansu kuma sai gashi ALLAH ya kawomu har gida”. Ba k'aramin k'ona ran innaro maganar tayiba (dama an kawomu nanne dankar bak'in su gammu balle su za6emu, amma kuma sai gashi sun gammu anan d'in. Anyi gudun gara kenan.....🤣🙊). Bamu tsaya sauraren abinda innaro zata ceba mukayi fitowarmu zuwa gida. Su Sa'eed sun gaida innaro, anan take tambayarsu kosun za6a acikin wad'anda sukaje gaishesu acan gidanmu. Sa'eed yace, “eh mun za6a Granny, amma wad'annan dasuka fita yanzu”. Caraf innaro tace, “ai wad'annan anmusu miji shiyyasa su basujeba, sai dai cikin wad'ancan”. Bahaka sukasoba, amma yazasuyi, sai dai har sukabar gidan basu sanar da wa suka za6aba. Koda muka sanarma innarmu cewa tayi babu ko mai, karma hakan ya damemu. ★★★★★★★★ Har tsawon kwana 5 babu wata magana data fito akan suwa bak'in suka za6a, su Abba basuce da kowa komaiba. Hankalin iyayenmu mata duk atashe yake, kowa takasa kunne taji wacece aka za6a, sai dai babu mai iya tunkarar iyayenmu maza da zancen, dan duk ba suga fuskar hakanba. Satinsu guda da zuwa saiga bak'i sunzo wai an kawo kud'in aure. Hankalin iyayenmu fa yakuma tashi, dan ganinsu wani munafurcin akayi shiyyasa aketa k'unbiya-k'unbiya. Nanfa suka shiga 'yan tsugunne-tsugunne Na gulma irinta gidan yawa. Kwana biyu dayin haka su Abba suka sanar da cewa nida Munubiya sukace sun za6a. Innaro ce tafara k'aryatawa, sannan tace, Sam bata aminceba, ina jikokin talakawa 'ya'yan bak'in haure suka kai matsayin auren 'ya'yan babban mutun irin sanata halliru, ai k'aryane sannan munafuncine, agabanta su Sa'eed sukace Zarah da Siyama suka za6a. (Zarah k'anwar ya hameed Ce, babanmu d'aya, Siyama kuwa d'iyar momy Hadiza Ce d'iyar dady). Jin wannan zance yasa kowa ya fahimci akwai munafunci a lamarin, kowa yasan yanda mamansu ya hameed suke da momy Hadiza a gidan, kansu had'e yake. aikam matan gidanmu suka harzuk'a sunata yada magana, harma abin yaso yazama fad'a, innarmu ce batace komaiba, ita cewama Abbanmu tayi dan ALLAH amaida zancen auren kansu Siyamar tunda innaro tace dama su suka za6a. Banza abbanmu yamata dan yasan innaro tayi hakanne danta k'untatama innarmu, amma tabbas dabakin su Sulaiman sukace 'yan biyunnan suka za6a, shin sai yaushene inna zata bar muzgunama Aisha da munanata a gidannan?, shekara kusan Arba'in ana Abu guda babu sassauci, tunda yake baita6a ganin rana d'aya da innarmu tama innaro koda kallon banzaba bare rashin kunya, sa6anin sauran matan gidan da basa kunyar ya6a mata magana koda ta habaicine. Kwana kusan hud'u ana d'auki ba dad'i akan wannan zance, saboda akawo k'arshen maganar sai Abbanmu yace su Sa'eed suzo su nuna wad'anda suka za6a da kansu. Hummm bamusan miya faruba, (konace mi innaro dasu momy hadiza suka k'ulla ba) munga dai sunta murnar zuwansu Sa'eed d'in, sai rawarkan had'a abincin tarbarsu sukeyi, dan ranar su biyu kacal sukayi, kuma abin mamaki wannan karon agidan innaro aka saukesu. Bayan isowarsu dakamar mintuna 20 sunci abinci sai akace duk muje gidan innaro. Su Haleematu duk sun rigamu tafiya, mune k'arshen zuwa muda Fauziyya, saidai muna shiga gidan Innaro ta samu mukabi ta k'ofar kitchen nida Munubiya kawai, Fauziyya kuma aka barta tashiga ta falo. Yanda sukaita zumud'in kallonmu wancan karon a yau ba haka bane, gaba d'aya hankalinsu Na kan Siyama da zahra, abin ya bamu mamaki har sauran 'yan uwanmu. Tunda mukaga haka duksai muka fice muka koma gida, su Haleematu harda kukansu, mukanmu zukatanmu sun sosu, dan harga ALLAH Sa'eed ya kwantamin arai. Wanan lamari saida yajawo gagarumin fad'a agidanmu irinma wanda ba'a ta6a yiba, dan saida takai matan gidanmu da 'Yar tone-tone asirinsu yanda suke kulle-k'ulle wani lokaci akan innarmu da junansu. Sosai ranar saida ran kowa ya 6aci, amma mamansu yaa Hameed da momy Hadiza su wasai sukejin kansu, koba komai sune a sama suke gani, 'ya'yansu zasuje gidan Hutu. Abbanmu yasamu innarmu yayta bata hak'uri, dan tabbas yanada tabbacin akwai lauje cikin nad'i akan lamarin, tunda su Sa'eed da kansune suka Samar masa za6insu, amma gashi a wannan karon since su siyama ne ba 'yan biyu ba. ALLAH sarki innarmu sarkin hak'uri, cewa tayi babu komai, dama can su Siyamar ne matansu, Dan haka tunran gini tun ran Zane, suma sauran ALLAH yabasu Na kwarai. Sosai Abba yak'ara jin jinama hak'uri da tawakkali irin Na matar tasa, abin sonsa, wadda yakejin har duniya ta tashi k'aunarta dabance a ransa, yana sonta harma baisan yanda zai fassaraba, kullum cikin mata k'yak'yk'yawar addu'a yake akan ribar hak'urin datakeyi da kowa agidan har mahaifiyarsa. yana ganin Kimar Aisha sosai da girmanta, tunda suke babu rana d'aya dazaice gawani abun aibu data aikata masa, sai dai abinda ba'a rasaba saboda zomu zauna zomu sa6a, balle shekara kusan 40 ba wasabace. ★★★★★★★ An tsaida bikin Siyama da Zarah dai-dai danasu aunty Hauwa'u, komai kuma ankawo, saura lefe da sadaki kawai. Ahaka muka koma makaranta inata yak'in fidda Sa'eed daga raina, ALLAH ma ya taimakeni dama bawai yashiga irin cancikin nan baneba. ****** Yau lectures d'in safe garemu, dan haka mukayi shiri da wuri nida Munubiya, a tsaitsaye mukasha kunun da innarmu ta dama mana, Dan yau girkin mamansu ya Hameed ne, idan bata gadama ba sai takai 8 bata kammala ba, har yara saisun makara, Aiyaan yashigo d'auke da lunch boxs nasu yana tura baki gaba. “kai kuma lafiya kake cuno baki uwa na agwagwa?”. 6ata fuska yakuma yi tamkar zai fasa kuka, ya zube lunch boxs d'in saman kujera “Aunty ba mama bace tace wai yau batayi abincin dazamuje dashi makaranta ba, hakama fa jiya abincin dare ta d'umama ta zuba mana, amma damukaje school saigashi a kulan Haneep Indomi ne da kwai”. Aryaan ya kar6e da cewar “ALLAH kuma aunty namu tsami yayi kafinma muci, haka mukadawo da yunwa”. tausayi yaran suka bani, Munubiya tace, “kuyi hak'uri kunji 2 d'in inna, watarana sai labari ai”. Kansu suka jinjina mata sukace “to aunty”. innarmu tana jinmu amma uffan bataceba. Fita nayi batareda nacema kowa komaiba, wani shago dake can k'asan layinmu naje, nasiyo musu yoghurt da cake k'ananu, nahad'o musu da biscuits. A harabar gidan Na iskesu harsun fito, sauran yaran sunata shiga school bos d'insu da ake kaisu makaranta. School bag d'insu nabud'e Na saka ma kowa nasa, sannan nace ayi karatu da k'yau kunji babys d'inmu”. Cikeda jin dad'i suka amsa min da fad'in “to auntynmu”. Kumatunsu Na sumbata sannan na taimaka musu suka shiga motar suma. Ina shigowa munubiya tamik'e tana fad'in “wai ina kikaje? kinsanfa jarababben lecturer d'inanne zai shigar mana yau”. “sorry sweetheart tashi muje”. Dubu 1 innarmu tamik'o mana, kar6a mukai muna mata godiya, muka fito tana binmu da addu'oin fatan alkairi. Mun lek'ama su Siyama, kowacce sai tace batada lectures d'in safe, fauziyya da Feedausi ce kawai muka tafi, dansu duk department d'inmu d'ayane..........✍🏼 One luv🥰🥰 *_ALLAH ka gafartama iyayrnmu👏🏻😭_* [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻5⃣ ...........Wajen 4pm muka fito daga cikin makaranta, mu 6 ne yanzu, sa6anin d'azu damukazo mu hud'u, bayan tahowarmu Safara'u da Haleematu suka taho suma, duk da mun rigasu gama lectures sai muka jirasu suka fito muka rankayo tare domin tafiya gida, bamu samu school bos ba, dan haka muka da6o sayyadarmu har zuwa babban gate, muna tsaitsaye abakin titi, tareda wasu daga cikin tsirarun d'alibai irinmu, tundaga nesa muka hango tahowar motocin da uban gudu, saika d'auka sukad'aine akan titin saboda gudun dasuke tsulawa tamkar zasu tashi sama. duk baya muka matsa, dan tabbas wad'annan suka sameka babu abinda zai hanasu takeka su wuce batareda sun damuba. Tamkar wucewar iska haka suka dinga gittamu, jikake shuuuu!! shuuu!! shuuu!!. Furicin wani mayshin saurayi dake jingine jikin motarsa yazo d'aukar wasu 'yan mata biyu dake gefenmu 'yan matan sunada jin kan masifa, ko'a makarantar bakowa sukema maganaba, department d'inmu d'aya dasu amma ko kallo basu isheniba, dan ko sallama bata ta6a had'ani dasuba.. Saurayin yabi motocin da kallo yana fad'in “tab ashe *_GALADIMA!_* yashigo gari kenan?”. “Da gaske yaa Usman?”. ‘d'aya acikin 'yan Matan tafad'a cikin matuk'ar zumud'i’. Yace, “da gaske mana baby, baga motocinsa kuna ganin sun wuceba”. Dan danan suka shiga murna, kai kace an musu albishir da aljanna ne. Baki na ta6e inajan k'aramin tsaki. Fiddausi tace, “to waye shi galadima d'in?”. “oho musu”, ‘cewar Munubiya’. Budurwar dake tsaye d'ayan gefenmu itada saurayinta suna jiran abin hawa suma tace, “Galadima d'an Sarki kenan, *Yarima Sameer!”*. “humm lallai kuce manyane, shiyyasa suke gudun da kosunbi takan talaka babu abinda za'ayi”. ‘cikeda 6acin rai nake maganar’. Dariya su siyama sukayi suna fad'in “toke ina ruwanki?, k'asarfa tasuce, sai yanda sukayi da ita, tsakaninmu dasu saidai mu hangesu cikin mota ko ranar hawan salla”. Dogon tsaki nakuma ja tareda kauda kaina daga garesu na maida hankalina wajen tare wata taxi dake gabatomu. A motama firar dasu Haleematu sukaitayi kenan, ta Galadima ne ko uwarmi ne ma Na manta. nidai uffan ban kuma tofawaba, hasalima haushi hirar tasu takoma bani, dan mai taxi d'in yasaki baki sai wani basu labarin Galadima d'in yakeyi dakuma kwarzan tashi, earphone na jayo a cikin lady's bag d'ina na manna a kunne danma nabar jinsu gaba d'aya. Saida muka iso gida sannan Fauziyya dake kusa dani ta zungureni, d'agowa nayi Na kalleta sainaga duk sun fice, bance komaiba nafito nima. Mun iske innarmu bata nan, saisu Aiyaan kawai zaune a falo suna kallo, shigowarmu yasasu tasowa da gudu suna mana oyoyo, muma mun taryesu da murnarmu, Munubiya tace, “Aryaan miyasa baku cire Uniform ba kukayi wanka?”. “yo aunty mun dawo munga Innarmu bata nanane”. Nace “innarmu bata nan? to ina taje?”. “muma bamu saniba aunty, munje kuma kitchen bamuga abinci ba, kuma yunwa mukeji”. Munubiya tace, “ya salam, kujira ina zuwa”. Fita tayi, babu dad'ewa sai gata tadawo cikin damuwa, ina cirema su Aryaan Uniform, Na kalleta ina fad'in “mike faruwa Munu...? Ina abincinne?”. Kwallar idonta ta share, ta zauna bisa kujera sannan tace, “naje mama tace wai innarmu ta d'auka abinci tatafi dashi hospital, dan haka shine rabonmu”. Raina a 6ace na mik'e zan fita, da sauri munubiya ta ruk'oni, “please Munaya, kibarta kawai, yakamata mu kira innarmu muji waye a hospital? Inaga wannan yafi komai muhimmanci nake gani akan abinda mamar tamana”. “Haba Munubiya, wannan wane irin rashin mutunci ne, wai mi Matan gidannan suke tak'ama dashine? Idan suna tak'ama da Ubanninsu muma ai nan gidan Ubanmune ko, yanzu ace yarannan kamar su Aryaan su dawo school tun 3 amma ahanasu abinci, wannan wane irin zaluncine? Kisakeni kawai naje naci kutumar uban matarnan munubiya, wlhy sai dai yau Abba yace nabar masa gidansa”. “A'a munaya, duk hakama bata tasoba, idan hankali ya6ata hankali ke nemosa, bai kamata mutaru muzama d'ayaba mu da su. bara kawai naje kicin d'in Na dafa mana wani abun mai sauk'i, kiyi hak'uri dan ALLAH, kinga innarmu bazataji dad'iba idan tatarar da faruwar hakan”. Badan raina yaso ba Na hak'ura, saman kujera nakoma Na zauna ina huci, nikad'ai nasan minakeji a zuciyata. Munubiya tafita dan nema mana abinda zamuci, nikuma Na d'auki waya domin Kiran innarmu naji abinda tajeyi asibiti. Harta katse bata d'agaba, nakuma kira akaro Na biyu sannan ta d'auka, gaisheta nayi da tambayar mitajeyi asibiti?. Daga can tace min Nafisar mama Rabi'a Ce jikinta ya motsa yanzu hakama jini ake buk'ata amma an Gaza samu, gashi yaa marwan dayakan bata jinin baya nan yayi tafiya shida Abbansu. Hankalina a tashe nace “innarmu ganinan zuwa yanzunnan insha ALLAH, kuna general hospital ne?”. “eh muna nan”. “ok insha ALLAHU ganina zuwa”. 'Dakinmu nashiga da Sauri nad'an watsa ruwa a tsaitsaye saboda naji dad'in jikina, komai ban tsaya shafawaba Na zira doguwar Riga jallabiya Na fice da hanzari. A k'ofar fita falo naci karo da munubiya d'auke da babban faranti tazubo spaghetti tanata turiri. namatsa baya da Sauri INA fad'in sorry, munubiya bara naje asibitin wajensu innarmu, wai jikin feena ne ya motsa kuma ana buk'atar jini, gashi yaa marwan sunyi tafiya da abba”. Munubiya tace, “toko Na juye mana abincin a kula mu tafi gaba d'aya?”. Nace, “a'a munu... Ki zauna dasu Aiyaan bara naje ni kad'ai, baikamata mubar wajen ba kowaba”. “to shikenan, yanda akayi ki ta6oni awaya, amma in kunkai dare zakuganmu muma, abincinfa?”. “humm munu bar abincinnan, banida wata nutsuwar cinsa, saina dawo”. Ban jira amsarta ba nafice. ALLAH ya taimakeni INA fita nasamu napep. Mintuna kad'an muka isa hospital d'in, kud'insa na biyashi nashige da hanzari ina k'ok'arin kiran innarmu. Babu dad'ewa kuwa ta d'aga, nace mata gani acikin asibitin. Kwatance tamin na inda aka kwantar dasu 6angaren masu sikila. A rikice na iske innarmu da mama Rabi'a, saboda jikin feena ya motsa mata sosai a wannan karon. Nace, “mama yanzu mi ake cikine?”. “Rashin jininne matsala yanzu Munaya, sunce kuma anemoshi da gaggawa, to dama can jinin Fadeel baya yimata shiyyasama ko gwadasa ba ayiba, Marwan dake bata kuma sunyi tafiya da abbansu”. “mama ina zuwa, bani takardar da suka baku”. Mik'omin tayi nafita da saurina. dukna rikice inata kai kawo dan ganin ansami jinin, amma har magriba ta rufa ba a samuba, saboda jinin feena yanada wuyar samu, ana cikin kiraye-kirayen sallar isha'i saiga Ayusher ta iso itama, dama an barta a gidane saboda babu kowa, to takasa hak'uri tabiyo sahu, da ita muka cigaba da shiga da fita, saida aka fito sallar isha'i ALLAH yasa aka dace da samun leda 1, saura 1, dama biyu suke buk'ata. ana cikin d'aura mata saiga Munubiya ita dasu Aryaan da kulolin abinci. Koda aka gama sakawa sai muka koma Neman d'ayar ledar data rage, yanzu harda munubiya muke tare. Muna a lab d'inne muna shawarar ko a d'iba namu jinin idan zaiyi babu damuwa. Takun takalman damuka jiyo yasamu juyawa harda likitan da maganarsa takatse bisa k'ok'arin bamu amsa dayakeyi. wani ni'imtaccen k'amshine ya iso hancinanmu tunkan mamallakin turarenma yakai ga isowa inda muke. d'auke kaina nayi na maida ga mai d'ibar jinin. Likitan naga yafara gyara kujera yana fad'in “dama yalla6ai ya shigo gari yau? Ni nama manta yaune ranar dayake bada jini”. Bai samu mai bashi amsaba a cikinmu har tawagar Wanda yakira yalla6ai suka iso wajen. Munubiya da Ayusher suka matsa gefe saboda wata uwar tsawa da masu take masa baya suka daka mana, nikam koma motsawa banyiba bare nasan ALLAH yayi ruwansu awajen, saima baki dana ta6e na d'auke kaina daga saitin dasuke. Bulala d'aya daga masu jajayen rigunan ya d'aga da nufin zubamun. “Wanda suke kira Yalla6ai dake zaune a kujerar da doctor ya ajiye masa ya d'agamasa hannu da Sauri, alamar karya dakeni”. Cikeda girmamawa yace, “angama zaki s.........”. Hannu Yakuma d'aga masa alamar baya buk'atar kirarin. Baki nakuma ta6ewa sannan na ra6a ta gefensu nafice, banga fuskar Yalla6ai d'in nasuba, saboda ya juyamin bayane ni, sananan shima tunda yashigo bai kalli kowaba a lab d'in, yanata aikin danna wayarsa, kuma baiyi magana ba, ko doctor da Norse's d'in da suka gaidashi hannu kawai ya d'aga musu, kuma ko d'agowa baiyiba yanata aikin danna waya kai kace zai danno hanyar zuwa aljannane aciki. Waje na dawo nayi zamana ina cigaba da game a waya, su Munubuya dai suna cikin, bansan uwarmi suka tsaya yiba awajen. Kusan mintuna 40 saigasu sunfito, takun takalmansu kawai naji, amma ban d'agoba, sai k'amshin turarensa daya cika illahirin wajen, saikuma gaisuwar da mutane keta faman zubewa sunayi masa, ko sau d'aya banji ya amsaba. Tsaki naja inamaijin haushin wannan mutumin, to wayema shine? dayakema mutane wannan jinkan., motsooww aikin banza kawai. Tabbas yaji tsakin da akayi, hakanne yasakashi d'ago k'yawawan idanunsa yakai duba saitin Inda yajiyo tsakin, akan *munaya* dake zaune bisa kujerun dake Jere awajen ya sauke su, sai dai baya ganin fuskanta sosai, saboda ta duk'ar da kai tana danna waya, kuma gyalen jallabiyarta yarufe mata Rabin fuska, ita kad'aice zatayi wani motsi awajen suji, dan tafi kusanci da Inda suke tsaye. Janye idanunsa yayi kawai daga gareta, yay saurin d'agama bayin dake k'ok'arin tafowa gareni hannu. Cikin Wata tattausar murya mai aji dake cike da k'asaitar masu isa najiyo yana fad'in “Bayta kawai”. Cikeda girmamawa bawan yace, “ya shugaba tsaki tayi fa”. Shiru yay kamar bazai tankaba, saikuma najiyo yace, “kasan dawa take?”. Bawan girgiza kai yayi alamar a'a. Bai sake cewa komaiba yay gaba suka bishi a baya. 'Dago ido nai nabi bayansu da kallo, sainaga sun nufi 6angaren mata masu haihuwa. janye idona nayi ina fad'in “kadaiji dashi Malam, kana fama da Girman kai kamar wani Sarki? Abinma dariya ko (R) bai iyaba, wai bayta”. Dai dai nan su Ayusher suka iso cikeda farinci, hannunsu d'auke da ledar jinin Cikeda jin haushi nace, “wai uwarmi kuka tsaya yi acikin lab d'inne?”. “Uwarmu ta gode”. ‘ cewar Ayusher’. Munubiya kuma tace, “zaman namu aiko yayi amfani, tunda gashi mun samo sauran jinin ko”. Na kallesu da mamaki, “ina kuka samo jinin kuma to?”. “Galadima ya bayar”. Cikin ta6e baki nace, “miye kuma Galadima? A inama kukaga wani Galadima kome ma kukace?”. “wanda yashigo muna cikifa, ai Galadima ne (Yareema Sameer d'an sarki)”. Ido na waro waje, “wai kuna nufin wannan mai shegen girman kai d'in dama shine Galadiman? kenan munu.... shine yawucemu d'azu munfito makaranta?”. “kwarai kuwa sweetheart shine, kuma wlhy bashida Girman kai kamar yanda kike zato ko Sis.. Ayusher? ”. “Wlhy kuwa hakane Munu..., ashe duk k'arshen ko wane wata saiyazo asibitinan yabada jininsa gamasu buk'ata, gashi jinin nasa mai irin wahalar samu d'inanne irinna feena, kai mutuminnan yayi wlhy, Sarauta ba karya baceba, danyau naga tsantsar sarauta da mulki da k'asaita ajikin Galadima, yanzu haka zai zagayane yaduba marasa lafiya”. Harara na ballama Ayusher daketa zabga surutu uwa aku, na warce jinin daga hannun munubiya ina fad'in “idan kun gama shirmen kwa taho”. Kallo suka bini dashi, Ayusher tace, “Anya yarinyarnan batada aljanu?, ke kowama bai mikiba?, yanzu nan duk had'uwar Galadima Munaya tana nufin bai burgeta ba kenan?”. Dariya Munubiya tayi, sis... Ayusher har yanzu baki gama fahimtar Munaya ba na lura, kyagama abinda yafi haka indai daga wajentane. Yanzu hakama tunda kikaji tace haka ko sau d'aya bata kalleshiba wlhy bare tasanma kalarsa. kinga muje kinji. “humm aiko wlhy inabata kalleshiba anyi babu ita kuwa, ruwa ta shata kuma, yo kobabu komai aina bada koda labarine nace nata6a ganinsa ido da ido ko”. ‘cewar Ayusher’. Dariya kawai Munubiya tayi, taja hannunta suka tafi. Sanda suka iso harma an fara k'ok'arin sakama feena jinin, dama wancan yak'are. Duk muna zaune a k'ofar d'akin bisa kujerun wajen, Aryaan da Aiyaan duk suna jikin mama Rabi'a barci ya d'aukesu, fadeel na kusada innarmu yanacin abincin dasu Munubiya suka kawo, zama nayi kusada fadeel d'in na saka hannu nad'au cokalin dayake cin abincin ina fad'in bro... nimafa yunwarnan nakeji, rabona da abinci tun kusan 1 danaci a kafteriya na makaranta”. Kallona yayi yana cewa “sannu da k'ok'ari sis...., shiyyasa gakinan tsula guda bak'ya gaba bakya baya keda munu....”. Cokalin nakai zan kwala masa a kai ya kauce yana dariya, nima dariyar nayi na d'auki kular abincin na k'ara mana. Muna cikin ci Ayusher ma tamatso tace zataci, munci mun k'oshi sannan muka gyara wajen, mama da innarmu ma sukaci, dan zuwa yanzu duk mun sami 'Yar nutsuwa. Kusan 10pm saiga Abbanmu shida baba k'arami, duk muka gaidasu suka tambayi mai jiki, innarmu da mama Rabi'a suka amasa musu da sauk'i. Har d'akin suka shiga, suka duba feena daketa barcinta, sannan sukace muzo mu tafi gida, za'a bar innarmu da mama Rabi'a su kwana. Saida safe mukai musu muka fito, Fadeel ya d'akko Aryaan, baba k'arami ya d'akko Aiyaan. Saida muka fara sauke Ayusher da Fadeel gida sannan mukuma muka wuce. Mun tarar gidan tsitt alamun duk anyi barci, saidai masu wayar dare da samari irinsu aunty Ramla, saikuma masu charts. Abbanmu da baba k'arami suka d'auki su Aiyaan, har d'akinsu suka kaisu sannan suka fita. Muma shirin barci mukayi muka kwanta cikeda kewar Innarmu, muna kwanciya muka kirasu da k'arajin mai jikin sannan muka tafi duniyar barci muma, dagani har Munubiya babu mai wani saurayin da zamu 6ata lokaci wajen yin hirar dare...............✍🏼 Kumuje zuwa my guys🤩👎🏻 Gobe idan ALLAH ya kaimu baza kujiniba, inada wani d'an uziri, sai Monday idan ALLAH ya kaimu kuma. https://chat.whatsapp.com/K1qwmMusX7ILDLATGSvfHJ *_RAINA KAMA........ FANS CLUB_* _Duk Wanda yasan yana karanta wannan buk d'in ya garzaya yanemi link Na RAINA KAMA FANS CLUB, a wannan gidan kawai zan dinga posting a halin yanzun, awannan karon bazan turama kowa buk ta PC ba, narigada nayi rantsuwa. Amma annan zaka iya samu da faro, sannan inhar ba'a tattaunawa akan novel d'in zanyi waje da mutum babu ruwana, kuma kar a turomin kowanne novels acikinsa Dan ALLAH, inba hakaba zan fidda mutum ko Yaya nake dashi🙅🏻, nabud'e gidanne saboda anan kawai zan dinga posting yanzu, sai wasu groups dabasu wuce 3 ba._ Ina fata zaku bani had'in kai please, inba hakaba ALLAH zai koma Na kud'ine saboda tsaro ba tsoroba😎🤣 One luv🥰🥰 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu👏🏻😭_* [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _____________ *_ASSALAMU ALAIKUM_* _Jiya da daddare akaita kirana mutane Na tanbayata Yaya jiki, tun ban fahimci maganarba hardai nafara tsarguwa nayi tambaya. Dan sai kira kan kira ake jeramin, wata take sanar dani taga wani posting ne yana yawo wai za'amin CS. babu shiri nabud'e data naga mike faruwa, group d'in farko dana bud'e sainaci karo da wannan posting d'in mutane nata comments, nabud'e nabiyu ma hakan dai._ *_Assalamualaikum Alaikum,Dan Allah kuyiwa billyn Abdul(ma rubuciyan RAINA KAMA. Adua'baby ya mutu a cikin ta zaa cire Mata Shi yanzu_* _sai daga baya nakejin Bily galadanci ce batada lfyar, amma wata ta maida zancen haka saboda sunan namu yazo d'aya, to ALLAH yabata lfy itama._ _sannan ina shawartar jama'a Dan ALLAH kuringa nutsuwa wajen tantance Abu kafin Ku yad'ashi, domin wadda tayi wancan write up d'in ta zaunane ta tsara nata son zuciyar, wadda tayi posting d'in farko akan ciwon Bily galadanci sunan Bily tasaka ba nawaba, itakuma ta canja nata tsarin tashiga ya d'awa, ALLAH ya shiryar damu, yakuma bama marasa lfyarmu lafiya._ *banyi niyar posting ba yau, amma ganin wancan write up d'in yana cigaba da yad'uwa yasani dole yi Dan na warware muku zancen.* ______________________________ 👉🏻6⃣ .......Bamusan abinda yafaruba, mukaji 'yan gidanmu suna k'ananun magana da safe, wai girkin jiya na dare da mamansu yaa hameed tayi sai asararsa akayi, girkin yay d'anye yak'i dahuwa, kuma a gas tayi girkin bare ace iccen yabata matsala, gashi kuma normal gas d'in yake aiki. Muna cikin yima su Aiyaan shirin school muka fara jiyo hayaniya, sai da muka gama musu shirin sannan muka fito, cirko-cirko muka iske 'yan gidanmu, yayinda mamansu yaa hameed keta zabga masifa. tana fad'ama abbanmu wai mune muka mata kwari shiyyasa jiya abinci yay mata d'anye danta hanamu abinci, kuma gashi yanzuma tasaka doya amai tak'i soyuwa. Ni dariyama taso bani wlhy, wai mune muka mata kwari, to miye kwarinne ma datake magana a kai? danni bamma sanshiba..... Maganar Abbanmu ta katsemin tunanina. “ 'Yan biyuna kuzo nan naji kunji”. K'arasowa mukayi kusada abbanmu harsu Aiyaan, ya kallemu cikeda kulawa, “haba 'yan albarka mike faruwa haka?”. Cikeda rashin fahimta nace, “Abba a ina?”. “haba twins d'in Abba, bakuji mi mamanku take fad'aba? abinci yamata d'anye jiya da yau”. “amma Abba Dan abinci yayi d'anye kuma sai ace mune? Kagafa jiya munama asibiti bamuci abincin dareba agida, darana ma mama hanamu tayi tace innarmu tatafi da kasonmu asibiti, haka muka dawo muka iske su Aryaan sunajin yunwa, sai Munubiya Ce tamana girki, kuma tayi takai mana wani asibitin, ni wlhy Abba bammasan wani kwari dasuke maganaba akai, wannan ai canfine, tunkuma zamanin da aka barsa”. “canfin uwarki, kujimin munafukar yarinya, inbakune kukayi muguntarba uwarwaye yayi, to wlhy ahir d'inku, ba 'yan biyu ba ko 'yan gomane ni ubanku zanci a gidannan.......” Afusace Abba yace, “to ai gani, saikizo kici ko, ai gaskiyama yarinyarnan tafad'a, wannan canfine kawai, dan abinci yayi d'anye saikuma a fassarashi dawani Abu daban, haba Dan ALLAH, saikace wata mara ilimin addini? Karna sake jin wannan maganar, inba hakaba rankowa zai 6acine a gidannan”. Yana gama fad'a yabar wajen. muma ganin haka muka tasa su Aiyaan gaba muka koma 6angarenmu. duk da nakasa fassara mi mama ke fad'i hakan yamun dad'i, koba komai dai ai ALLAH yamana sakayya da hanamu abinci datayi muda wad'anan k'ananun yaran da basu da alhakin kowa. Yanzuma munubiya Ce ta dafo mana indomi mukaci, sanan ta zubama su Aiyaan a kulolinsu Na makaranta, suna tafiya muma mukayi shirin tafiya School. Bamu tsaya jiran sauranba mukayi gaba saboda zamu biya ta asibiti, kuma munsan acikinsu babu mai binmu, harmun fita saiga Fauziyya tabiyomu, itama zataje taduba feena d'in. Alhmdllh munma tarar an sallamesu sunata shirin tafiya gida, mukaima feena sannu, ta amsa tana fara'a da tambayarmu ya makaranta?. mukace gatanan zamu tafi. Bamufi mintuna 30 ba muka fito, Fadeel ya d'aukesu, mukuma muka wuce school. A mota Munubiya take bama Fauziyya labarin ganin Galadima damukayi jiya a asibiti, ko sau d'aya ban saka musu bakiba har muka sauka. ★★★★★ A wannan karon har mamansu yaa hameed tagama girkinta Na kwana biyu asarar abinci akaitayi, Dan kullum d'anye yake mata. hakan yasa taita sakin habaici agidan itada muk'arrabanta irinsu momy hadiza,. Maman Fauziyya ta sanar ma innarmu komai tun randa taje duba feena agidan mama Rabi'a, Dan haka Innarmu tayi kunnen uwar shegu dasu, tamkarma batasan da ita sukeba balle ta nuna tama fahimci zancen nasu. Innaro ma tazo tayi tata tsiyar San rai, tabi duk ta zagemu dacin mutuncin innarmu, koma fitowa innarmu hanamu yi tayi, har Innaro tagama tafice. Matan gida najin dad'i. ★★★★★★ Haka rayuwar tacigaba da tafiya, yau da gobe kayan ALLAH har gashi azumi ya rage saura kwanaki uku kacal a fara, Dan haka musulmai NATA shirin tarbar wannan wata mai tarin albarka da falala. Kasuwanni sun cushe saboda yawan hada-hada, duk da 'yan kasuwa sunyi taiyar tasu ta k'arama abinci kud'i, maimakon su sassauto bayin ALLAH su sami sauk'i (ALLAH ka shirya 'yan kasuwarmu subar wannan hali dai). A 6angaren gidanmu ma iyayenmu maza duk sunyi shirin, Dan dukkan wani abun buk'ata an tanadeshi, sai abinda ba'a rasaba dazai iya lalacewa idan an ajiye, wannan anbarsa yayunmu maza su ringayo cefanensa kullum kamar yanda aka saba. Itama Innaro an ajiye mata dukkan abinda zata buk'ata, dukda kullum daga gidanmu ake kaimata abinci, safe yamma da dare, kuma dolene kowane 6angare sai sunkai nasu. Muma a 6angarnmu munyi dukkan namu shirin, dukda abin zai had'e mana da zuwa makaranta, hakan yasa nake tausaya mana, gashi ana tsula rana mai zafi kuma. Alhmdllh yau ta kasance Alhamis, kuma yaune ake saka ran ganin wata atashi da azumi washe garin juma'a. Har zuwa 9pm kunnen kowa naga redio da talabijin, jira kawai Muke muji sanarwa daga sarkin musulmai. sai wajen 9:30pm sanan aka Sanar da ganin wata, duk wani Muslim yana cikeda d'okin fara azumin watan Ramadan da zamu Shiga goma ta marmari (inji hausawa😂). Tun alokacin duk muka d'auki niyya, kasancewar girkin innarmu ne tayi shirin tafiya d'akin Abbanmu, muma tace mu kashe TV muje mu kwanta kar atadamu da asuba kuma muzo muna k'unk'uni. Badan mun soba muka kashe mukaje mukai shirin barci muka kwanta da addu'ar abakunanmu. Aiko da asuba dak'yar innarmu ta iya tashinmu mukai sahur, tea kawai muka shama, dama mu bama sahur da abinci nida munubiya, garama ita wani lokacin takan had'a da kunu ko fura. Bamu kwantaba saida akayi sallar asubahi, still kwanciya muka kumayi, sai 8 innarmu ta tadamu, kasancewar yau saima 10 mukeda lecture, kuma zamu fito 12 ne. Tunkan aje da nisa azumin yafara garani, dak'yar Na daure aka kammala lecture muka fito, amma badan Na fahimci komaiba nidai yau. Su Munubiya sai dariya suke mini wai Raguwa, nidai ban kulasuba, Burina kawai naga mun Isa gida Na kwanta. Tunda muka dawo school nazube a falo k'asan carpet, ban sake Sanin duniyar danake cikiba saida munubiya ta tadani nayi salla, Ashe harsu Aryaan sun sako masallacima inata barci, sallarma dak'yar nayita atsaye, INA kammalawa nakuma kwanciya. “oh ni Aisha, wai Munaya mikikeson maida kankine? yanzu azumin kikema langa6e haka? saikace yau kika fara azumi a rayuwarki?”. “ALLAH innarmu bazaki ganeba, nidai ALLAH yasa akira salla da wuri”. Munubiya dasu Aiyaan suka sakamin dariya. “Aunty yanzufa k'arfe 2 ma, sauran kusan awa 5 dawani Abu asha ruwa”. ‘Aryaan yafad'a yana dariya’. Harara Na Dalla masa INA fad'in “ALLAH inbaka rife wannan bakin naka mai gajerarrun hak'oraba zaka dakune, Dan k'aniyarka kaiba yanzu kagama lodama cikinka abinciba?”. Aunty nimafa Dan innarmu bata tadamu baneba kawai, amma insha ALLAHU gobe zamuyi ko Aiyaan?”. cikin zumud'i Aiyaan yace, “eh mana, muma zamuyi bro”. “kuma wlhy yaro bai Isa karyashiba, garama karku d'auka”. Munubiya tamik'e tana dariya, “imm innarmu bara kiga naje nafara rage aikin, miza'ayi?”. “ki fere doya kafin Na fito, Munaya tashi maza kuje, kekuma ki gyara kayan miya”. “wayyo innarmu ki tausaya min mana”. “mukuma mu kashe kanmu tunda bama azumin ko?”. ‘cikeda gatse tayi maganar’. “a'a innarmu, bara naje kodaga zaune sainayi”. “kimayi daga kwance, raguwar banza kawai, ai mijinki yashiga uku, wataran sai yadawo aiki baki gama abinciba”. Baki Na tura gaba sannan nafita. Mun rage aiki sosai kafin la'asar, sai bayan sallar la'asar d'in 'yan Matan gidanmu suka shishshigo kitchen d'in kamar yanda aka saba, dama duk shekara gaba d'aya muke had'uwa a kitchen d'in 6angarenmu ayi abincin bud'a Baki, saidai saboda munada yawa akanyi time table saboda a rarrabu kowa da ranar da Zai taya mai aikin ranar. Da yake aikin yawane dandanan muka kammala kafin 6, a can tsakar gida aka shinfid'a manyan tabarmi bayan an tsaftace wajen, duk azumi gaba d'aya muke had'uwa asha ruwa dama anan, kafin matar ya hameed ta rasu har itama anan suke zuwa suyi bud'a Baki. Bayan mun had'u mun gama shirya komai kowa yanufi 6angarensu ya watsa ruwa kafin akira salla, dolene kaga jama'ar gidanmu aranar mu burgeka, babu fad'a babu hantarar juna, (yo kowa azumi yagama cin k'aniyarsa🤣🤪). Kasan cewar babu wuta ya kamal yazuba fetur a Gen... Ya tada, kowa yayi wanka saiyayi shirinsa da alwala yadawo tsakar gida ana jiran kiran salla, yara dabasuyi azumi baneba suketa shargallensu a tsakar gidan. Yanda na zube a tabarman tamkar mara kashi yasaka yaa Shafi'u fad'in “kai kekam anyi raguwar yarinya wlhy, nasan dai Munaya Ce, Dan Munubiya tafiki jarumta”. Dariya wad'anda ke wajen sukayi, yaa Naseer yace, “gaskiya mijinki yaga banu, yo idan yayi wasa dai bazai dinga cin abincin bud'a bakiba a gidansa”. Cikin dariya Aunty Hauwa'u ke fad'in “sai ya d'auka mata 'Yar aiki ai”. Caraf maman Safara'u ta amshe zance... “yo basai idan mai halin d'aukar 'Yar aikin bane, ana fama da masarar tuwo da shinkafa a jajibo mai aiki?”. Gurin tsit yayi kamar ruwa ya cinyemu, da alama kowa baiji dad'in furucin Na maman safara'u ba, sai mamansu yaa hameed ce tayi dariya itada momy Hadiza. Ganin abin zai koma cin zarafin juna sai maman fauziyya ta d'ako wani zance, daga nan aka koma hirar d'inkin salla. babu dad'ewa ma aka kira sallar magriba, cikeda d'oki kowa yafara k'ok'arin cin dabino. tab aini kam bandani, tuni Na d'ebi ruwa mai sanyi nafara sha, Dan shine babban burina. a gida mukayi jam'i, baba k'arami yajamana limanci. da ganan kuma kowa ya maida hankalinsa wajen bud'a baki, harda su hajiya innaro😕, tayi kane-kane ita masu gidan 'ya'ya😏, koda wasa dagamu har innarmu babu Wanda yashiga sabgarta gudun gwalasa, har aka gama lafiya muka gabatar da sallar isha'i da asham. daga nan aka d'an ta6a hira kowa yahad'a kan 'ya'yansa zuwa 6angarensa. haka muka cigaba da gudanar da ibadar azumin watan ramadan, tun ina ragwan taka harna fara daurewa, an gama goman farko aka shiga ta biyu (goma ta wuya🙊 ). Gaskiya nad'an wahaltu a tsakanin, ga makaranta ga aikin gidanmu dabaya k'arewa, ko wanke-wankema ya isheka, dukda had'uwa akeyi anayi kuwa. Azumi yana 13 aka kawo kayan sallarmu, an bajesu tsakar gida kowa ya za6a, kala uku-uku ne dama duk shekara, atanfa, shadda, les, saikuma iyayenmu mata su k'ara mana gwargwadon abinda ALLAH ya hore musu. Munada telolinnmu masu mana d'inki iya 'yan gidanmu kawai, shiyyasa bamuda matsala. Washe gari kuwa sukazo suka gwadamu, kowa aka saka sunansa ajikin kayansa da style d'in data za6a. Innarmu ma sun saya mana itada mama Rabi'a, dan tunma kan azumi an kammala mana d'unkunanmu mudasu feena, (innarmu tana business itada mama Rabi'a) shiyyasa duk wani abun kwalliya Na 'yan mata bama rasashi, duk da dai 'yan gidanmu suna mana d'agawar sun fimu komai, saboda danginsu masu kud'ine, suna ganin kayansu sunfi namu tsada. hakan baita6a damunmu ba, dan aganina duk sutura sunanta sutura, yawan kud'in nawani bai d'ad'ani da k'asaba, to barema Munubiya da babu ruwanta. Ana cikin haka muka shiga goman k'arshe Na azumi (goma ta d'okin sallah🤪😂). Ranar wata weekend yayyanmu maza suka kwashemu domin za6o takalma da sauran tarkace Na kwalliya, dama duk ankai yaran suma kowa ya za6o, mu matasan 'yan matan muka rage dakuma yayyenmu su Aunty khaleesa. Plaza ce babba mai k'yau da burgewa, kayansu Na manyane, amma yayyenmu dayake sunaso mufito suka kaimu can, sa6anin da da ake kaimu kasuwa kamar sauran yaran, su aunty khaleesa ne kawai ake kawowa nan saboda sune manyan 'yan mata, to yanzu muma mun shigo layi💃🏻. Sosai muka rikice da tsarin wajen, takalmane 'yan waje wad'anda duk inda kayi taku sai an kalleka ansan kagama Isa. Harda bags, kayan makeup, turarurruka da dogayen ruguna irinsu Arabia's gowns, gyalilla da kayan 'yan kunne, kananun Maya Na garari Na mata da maza, kai inaga babu abinda zakazo Baja sameshi awannan PLAZA d'inba kam”. Lallai an narka dukiya a wannan waje, ko plazan wanene? oho. munga dai sunan plaza d'in *BIRNIN GAYU!!* “Lallai kuwa taci sunanta birnin gayu”. ‘ cewar Anty Ramlah’. Haleematu tace, “wlhy wannan ace plaza d'in mijinace to bazan maimaita kaya sau uku ba, hakama waya duk wata za a dinga canjamin”. Dariya tabamu, dan haka muka shiga darawa kuwa. kowa yad'auki abunda yakeso gwargwadon iko, yayyanmu suka biya da kud'in dasu Abba suka basu, sannan suka cika mana danasu kud'in, kowa yafito cikin farin ciki muna jera musu godiya, mun d'auki picture's sosai awajen kuwa. muna tafiya a mota nake cewa yaa Anas dan ALLAH wai Plaza d'in waye wannan?”. “ai plaza d'in ta babban kwaroce k'anwata, plaza d'in *GALADIMA* ce”. shiru nai kamar banjishiba, danjin sunan wanda ya ambata, inada tabbacin kuma wannan mai girman kan tsiyar yake nufi kenan, yayinda 'yan uwana suka rud'e da firar galadiman. d'an tsaki naja nace, “ashema Na mai shegen girman kai d'innan ne”. Kusan atare sukace ke a ina kika sanshi? dahar kikasan yanada girman kai”. Shiru namusu, sai Munubiya ce tashiga basu labarinsa da had'uwar damukayi a asibiti da shi, aikam duk sai sukabi suka rikice, harda masu fatan yazame musu mijin aure. bansan miyasa duk hirar tasu ta k'untataniba, tabani haushi, saina maida hankalina ga kallace-kallacen jama'ar daketa kai kawo akan titi. Har mukaje gida suna hirar Galadima sudasu yaa hameed dake basu labarin halayen kirki Na Galadima d'in, wai kuma bashida girman kai kamar yanda Na fad'a, kawai dai dan ban fahimcesa bane nima. Nidai jinsu kawai nakeyi, amma badan Na yarda baida girman kai ba, tunda da idona Nagani ba labari aka baniba.😏ehe Innarmu tayi mamakin wad'annan kanya, dan haka takasa hak'uri, har 6angaren samarin gidanmu taje tamusu godiya da fad'an d'awainiyar tayi yawa ai, ga hidimar biki Na tunkarosu. Sunji dad'i sosai akan hakan da innarmu tayi, koba dad'i kowa yayi aikairi yanaso anuna jindad'i kuma amasa godiya. Sukace tayi hak'uri, ai k'annensu ne, idan basu mana ba wazai mana, da samari suzo suna mana hidima su lalata mana rayuwa ai garasu sumana su kare mutuncinmu. Sosai innarmu ma taji dad'in furicinsu, dan hakan ya nuna cewa su basu d'auki halayen iyayensu mataba Na raba d'aya biyu. Salla nata gabatomu, yayinda aka fara 'yan kimtse-kimtse Na shirin bikin sallar, masallatai nata rufe tafseer, hakama gidajen redio dana talabijin..............✍🏼 *Kusaka yayan mahaifiyata a addu'arku, ALLAH yamasa rasuwa ranar alhamis😭👏🏻, ALLAH ya gafarta masa, ya raya abinda yabari.* _Bansan makaranta Raina kama.... kunada yawa hakaba wlhy, nazata ki rabin group bazaku kaiba🙆🏻, gashi yacika wasu basu sami wajeba kuma._ Na gaisheku k'yauta, ina fatan duk kuna cikin k'oshin lafiya kuda iyalanku🤝🏻😊?. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*.👏🏻😭 [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻7⃣ .......Yau ake saka ran ganin wata, dan haka kowane gida zaka iya jiyo kamshin miya dana nama, harma da kayan snacks. Muma agidanmu kusan hakanne ta kasance, dan kowanne 6angare sunata hidimarsu, yau ko bud'a baki bakowa yasamu zaman yinsa ba. Muma muna namu 6angare muna taya innarmu ayyukanta, dayake kowa yana miyarsane, da safe ahad'u ayi tuwo da masa da shinkafa, haka muke had'a kalolin abinci iri-iri saboda yawan jama'a da gidanmu kan tara a ranar salla, abokan yayunmu maza, abokan su abbanmu dawasu dangin iyayenmu mata. Har wajen 10 munata aiki, sai kuma a lokacinne mukaji ana sanar da ganin wata. Nannafa yara suka shiga murna gobe salla, Muma kanmu manyan murnar mukeyi. badan mun kammala aikiba muka kwanta. Washe gari tun kiran sallar farko aka tadamu muka fara aiki, sai wajen 7am muka samu kanmu, a gurguje muka fara wanka da shirin tafiya idi, duk shekara dama 'yan gidanmu a masallacin da sarki yake salla muma mukeyi. A gurguje duk mukaita fitowa saboda horn da yayyenmu suketa mana, yara an d'urasu a school bos d'insu Na makaranta, yayinda mukuma muka rarrabu a motar yayinmu datasu Abba dasuka bayar, tunda bakowa keda motarna acikin yayyen namu. Dagani har Munubiya cikin shigarmu muke iri d'aya tamkar yanda muka saba a koda yaushe, dai-dai da kwalliyama iri d'ayace a fuskarmu, komai namu mukayishi iri d'ayane, wannan yasaka ake gaza banbancemu akoda yaushe. Mun Isa filin idi, inda muka taddashi dank'am da jama'a maza da mata, wasu harda iyalansu, kamar yanda muma muka taho baki d'aya harsu innarmu, mu mata muna 6angaren mata, yayinda mazan sukayi nasu 6angare. Khud'ubar da aka gabatar tazamo mana mai ratsa jiki da 6argo, Malam yayita cikin tsantsar larabci, yayinda wani malamin ya fassara acikin harshen Hausa, saboda marasa jin larabcin irinsu o e🙊. Daga nan aka gudanar da sallar idi kamar yanda addini ya koyar. Had'a kan yaran muka shigayi gudin karsuyi wani waje, sai dai hakan bata samuba, dan annemi Kamal da Haneep an rasa, nannafa muka shiga bulayin nemansu, duk mun rikice, gashi baba k'arami da Abbah sai fad'a suke wai sakacinmu ne. Tamkar zan kifa haka nake tafiya da sassarfa ina kalle-kalle. ban ankaraba naji naci karo da Abu, tunkan inkai idona kansa k'amshin turarensa yabigi hancina. da sauri na ware manyan idanuna bisa kamilalliyar fuskarsa dake d'aure babu alamar yasan miyema dariya, janye idona nayi cikin fargaba da fad'awa kogin tunani, inban mantaba irin wannan k'amshin naji a asibiti wajen Wanda aka kira galadima a wacan ranar da feena batada lafiya. Cikin yanayin tantama Na maida idona nad'an saci kallonsa... Tsaye yake kyam tamkar dutshin da aka dasa waje d'aya, idonsa akan wayarsa dake k'asa a tarwatse, Wanda inada tabbacin karon damukacine yasaka wayar fad'uwa. A rikice nace “ya Salam” tareda duk'usawa nafara harhad'a wayar. A hankali ya durk'usa kamar yanda nima nayi, ya d'ora hannunsa akan wayar dana ke k'ok'arin sakama battery ya zareta daga cikin hannuna. bugun zuciyata yak'aru saboda tsoro gashi yak'i cewa uffan, nasan nice da laifi, kafin Na ankara ya sake d'oramin wayar bisa hannuna yamik'e yabar wajen. Sororo nabisa da kallon mamaki da al'ajabi, sanye yake cikin farar shadda k'al, wando da riga harda malun-malun, ya murza hularnan da ake kira Minister bak'a a kansa, takalminsa da agogonsa duk bak'ak'e, duk da bawani k'are masa kallo nayiba fuska da fuska nasan tabbas yayi k'yau, kayan sun maidashi wani babban mutum. Ajiyar zuciya Na sauke saboda ya 6acema ganina, nabi wayar daya barni da ita a hannu da kallo, tomi yake nufi da hakan?. Banida mai bani amsa, dan haka nacigaba da had'a wayar, sai alokacin Na lura da sim card d'insa dake kan wayar yacire d'azun lokacin daya kar6a kenan. Jujjuya wayar nashigayi cikin tafin hannuna, wayace mai azabar k'yau ga k'amshin turarensa ya manne jikin wayar tamkar itama ana fesa matane. 'Yar tsagewane tayi kad'an daga gefe, amma daga hakan ni banga wata matsalaba, kenan yana nufin koyaya waya ta tsage a hannunsa tatashi aiki a garesa?. Nanma babu mai bani amsata. Cikin mak'oshi Na furta to wanene wannan d'in shikuma?”. “Galadima!”. ‘naji wata murya tafad'a abayana’. Cikin hanzari najuyon dan inga mai bani amsar tawa. wayam naga babu kowa, sai alamar gittawar mutum mai jajayen kaya. Goshina Na dafe inamai runtse idanuna, cikeda mamaki nace, “kenan shine wanda yabama feena jini? Galadima!”. Nafad'a cikin bud'e idanuna inabin inda yabi da kallo tamkar zan sake ganinsa, a hankali nakuma furta _“Galadima!”_. “galadima kuma?”. Najiyo muryar Safara'u a bayana, da sauri a cusa wayar cikin hijjabina Na mik'e, kallonta nayi cikin basarwa nace, “ya angansu ne”. Tace “eh mana an gansu tun d'azun, saikuma aka koma nemanki, miya faru naji kina kiran sunan galadima?”. d'an guntun tsaki naja “naji wasu 'yan matane suna fad'in wai INA zasuga Galadima, tunda ance yazo sallar idi. shine nikuma nake maimaita sunan Galadiman saboda takaicinsu”. Dariya Safara'u tayi, ke 'Yar uwa karkiga laifinsu wlhy, koni zan sameshi saina bar Sadeeq wlhy, yanzu fa Nima ake nunaminshi, dama haka yahad'u? Wayyo ALLAH yau naga tsantsar gwanzartakar sarauta ajikin bawan ALLAH nan, tafiyarsama kawai abin kalloce, inaga kuma yayi magana?, kai ALLAH yakai damo ga harawa...... kedai kawai........ Baki kawai Na ta6e, batareda nagamajin k'arshen zancen nataba nayi gaba abuna da mamakinta a raina, wai zata iya Barin sadeeq?, saikace ba'akan sadeeq d'in bane akaso cin zarafina da innarmu, amma yanzu saboda taga Wanda ya fishi bakinta yake furta haka. Da gudu Safara'u tabiyoni. Kusan a tare muka k'arasa Inda motarmu ta tsaya, yaa hameed yafara zagina akan INA kuma naje Na tsaya?, hak'uri nabashi muka Shiga mota kawai, dan nasan shima d'in masifafene kamar su abbanmu. Amotar ana fira amma ni tunanina yanakan had'uwarmu da Galadima ta yau, ga mamakin wayarsa daya bari yatafi a hannuna batareda yace min uffanba, kai wannan Bawa yanaji da k'asaita da mulki. Har muka Isa gida bakina bai iya furta komaiba acikin hirar tasu. Mun tatar su innarmu ma harsun huta su, yara kan summa fara cin abinci. Ban zauna faloba kamar yanda munubiya tayi, saina zarce bedroom d'inmu Na 6oye wayar sannan nacire hijjab d'ina nashiga bathroom Na wanke hannuna gudun kar wani yaji k'amshin turaren saina dawo falon. Tuni gidanmu ya kacame da hayaniya, munubiya tazubo mana masa da fankasu zamu faraci Ayusher da Feena suka shigo da gudu, juna muka rungume muna murnar ganinsu, Yaa Fadeel & yaa Marwan suma suka shigo, sai mama Rabi'a dake take musu baya tana rik'e da hannun Ahmad. Nan muma muka kacame da farin cikin ganin 'yan uwanmu wad'anda bamuda kamarsu, innarmu ta baje mana abinci da kayayyaki da dama dansu duk ta tanadesu, sai makwafta dasuke gaisawar arzik'i suma duk tabada ankakkai musu. Bamusan hidimar da kowa keyi anasa 6angarenba, mudai namu muka sani. Ayusher takawo bakinta saitin kunnena, ahankali ta rad'amin sweet sis.... Wlhy k'amshin turaren Galadima kikeyi, kinsan har abada bazan mance k'amshi nan ba”. Cikin dakiya Na d'ago kai Na kalleta tareda balla mata harara, “Ayusher wlhy ki kiyayeni, a'a k'amshin turaren sarki kikaji bana Galadima ba k'arewa”. dariya ta sanya harda rik'e ciki, nikuma Na tashi Na canja waje ina mamakin Ayusher mai gani har hanji, duk dawanke hannuna danayi sosai amma ace wai har yanzun anajin k'amshin turaren?, kai shikam wannan dawane mayen turare yake aiki haka?”. Wajen 12 muka fito domin zuwa kallon sarki dazai wice yima governor barka da salla. A wannan karan tafiyarmu daban data 'yan gidanmu, dan mafi yawancinsu duk sun fice gidajen kakanninsu, tacan masu ra'ayin zuwan suma zasuje. Mukuwa mudasu yaa marwan muka tafi. Acikin gari duk inda ka kalla jama'a ne keta kai kawo, musamman yara da 'yanmata da samari, kowa yaci kwalliya ta kece raini da garari (yo dama ai ance ba'a za6ar budurwa ran salla, saboda duk k'azantar mutum ranar saika sameshi cikin tsafta da gayu😂). Dukda akwai rana hakan bai hanamu jeruwaba domin kallon wucewar mai martaba sarkinmu da jama'arsa. Masu busa algaita da kid'an taushine suka fara wucewa, sai kuma ga tawagar sarki Na biye. tawagar saiki Na wucewa sai ta Galadima, kamar yanda mukaji wasu gungun samari Na fad'ar cewa ga Galadima nan. Kowa yasan dama tsarin haka yake, daga sarki sai shi. 'Daga idanuna nayin donson sake ganinsa a karo na biyu. yanzu kam ya canja shigarsa zuwa milk coulor d'in janfa da wando Na lallausan yadi, Wanda aka k'awatashi da d'inkin surfani Na ainahin gidan masu sarauta, ya d'ora Brown Na alk'yabba mai kwalliyar Milk Color, hakama rawaninsa daya zagaye fuskarsa ya kasance milk ne, takalmansa heir cover masu lankwasa daga gaba irinna sarauta, sukuma Brown. yanzun kam fuskarsa d'auke take da k'asaitaccen murmushi mai kama da anmasa dole, hannunsa d'aya dayake d'agama mutane yana d'aureda farin agogon azurfa, sai zabba biyu a yatsunsa Na tsakkiya Wanda nake k'yautata zaton azurfane suma. Nanfa su Ayusher suka fara d'aukarsa hotonsa a wayoyinsu. Tsaki naja ina hararsu, “mtsoww wahalallu kawai, dama kanku kuka d'auka yafi Ku k'are wajen d'ura hotunan Wanda baisanma da zamankuba a wayarku”. Kafin cikin su Ayusher wata tabani amsa, wasu 'yan mata dake kusadamu d'aya ta kar6e da fad'in “k 'yan mata kama kanki, kodai kema son nasa ne yakaiki ga kishinsa?”. Wata wawuyar harara Na buga mata, “kekuma shasha waya sako bakinki?, kajimin ballagaza kawai, uwarmiye abin so a jikinsa dahar ya isa ayi kishinsa? Ke dai dabakisan inda ke miki k'aik'ayiba ita dakon wahala, dan nakula ke amatanma suffar mata maza ALLAH yayiki....” Gaba d'aya suka taso min da masifa tamkar zasu cinyeni d'anya itada k'awayenta.. Yaa marwan dake zaune saman mota a bayanmu duk yana saurarenmu yad'ago kai ya kalleni, yasan tabas Munaya ce, baya buk'atar k'arin bayani kuma ko tambayar wacece ita, tunda Na nuna halin nawa, yace, “K munaya zoki shige mota”. Nasan halinsa sarai baya wasa damu, cikin tunzura baki gaba nazo nashige motar Na zauna, amma saina bar k'ofar abud'e k'afafuna awaje, banida buk'atar cigaba da kallon kuma, dan haka nabud'e data nashiga chart kawai ina cika ina batsewa masifa nacin raina, gashi kuma an hanani amayar da'ita,. sai antayama yaa Marwan harara nakeyi ta gefen ido baima San inayiba, gaba d'ayama sainaji dama banzo kallon hawanba. Koda muka bar nan ba gida muka komaba, yawo yaa Marwan yaytayi damu gidajen dangin babansu, bamune muka dawo gidaba sai magriba, kowa yayi ti6is da gajiya. Mun tarar innarmu da mama Rabi'a sunata shan hirarsu ta zuminci. Sai kusan 10 suka bar gidan. ★★★★ Washe gari muma agidansu mama Rabu'a muka yini har innarmu, koda yakema fitarmu mukayi nida Munubiya, Feena, Ayusher, mukabar su mama agida dasu Aryaan. Yauma mun zaga gari sosai, dan Ayusher takira mana wani saurayinta yazo ya kwashemu, yauma munje munga hawan sarki da la'asar, saidai yau babu Galadima a tawagar, hakan bai dameniba, dan nama manta da lamarinsa ni. Kwanaki kusan biyar zuwa 7 munashan shagalin salla, munsha yawo tamkar bamuda mafad'i mudasu Ayusher, sai Fauziyya dakan bimu wani lokacin idan basu fitaba da mamarsu suma. 'Yan matan gidanmu kowa sabgar gabansa yayi, rana d'ayane muka fita gaba d'aya domin gaida danginsu Abbanmu da Innaro takafa ta tsare akan sai munje wai su Anty Ramla sunyo musu sallamar aure. Kwanaki 10 cif dagama bikin salla muka koma makaranta. Haka rayuwa tacigaba da shud'ayawa, yayinda 'yan gidanmu keta shirin bikin 'ya'yansu, shiri akeyi babu kama hannun yaro, kowa burinsa ace 'ya'yan d'akinsa sune Star's, kuma sunfi kowa komai. Sati uku kacal bikin yarage, an kawo lefe daga gidan senator halliru, akwatina 24, siyama 12 Zarah 12. Humm ai ranar munsha kallo Na al'ajabi wajen mamansu yaa Hameed da momy Hadiza, habaici da gugar zana da burga, kowa yashashi, har dai abin yak'ure mamansu haleematu da maman Safara'u suka tanka musu, kafin kice mi gida yagama kacamewa da hayaniya, kowa yana ya6ama kowa magana, saida suka gama cin zarafin junansu sannan sukayi shiru bisa tsawatarwar baba k'arami, dayake yana gida a lokacin. An bar maganarne kawai amma badan ta k'areba, mudai a 6angarenmu ma innarmu hana kowa fitowa tayi, dayake weekend ne. Suma sauran duk an kawo nasu lefan, Aunty Rahaima, Ramlah, Hauwa'u sai aunty khaleesa, suma dai Alhmdllh, komai sai dai mak'iyi, duk da basukai nasu siyama ba gaskiya. a wannan karonma dai saida akayi 'yan gulmace-gulmace a gidanmu, amma basu bari tafito sarariba. Suma su yaa Hameed aka kai nasu lefan gidajen matan dazasu aura shida Ya shafi'u da yaa Nasser. suma iyayenmu sunyi k'ok'ari wajen had'a musu lefen girma, ankai kuma kowa Na sambarka. Tun bayan gama kai lefe gidanmu yakuma d'inkewa da k'us-k'us na gutsiri tsomar gidan yawa, kowa yana gulmar kowa akan aga wace rawa zaka taka, su 5 masu aurar da 'ya'yan. Mamansu yaa hameed zata aurar da 3, yaa hameed, aunty khaleesa da Zarah. Sai maman Haleematu zata aurar da aunty Hauwa'u. Sai Momy Hadiza zata aurar da Siyama da aunty Raihan. Mama Ruk'ayya kuma zata aurar da yaa Shafi'u da yaa Naseer. Maman Safara'u kuma Aunty Ramlah. Innarmu da maman Fauziyya ne kawai bazasu aurar da kowa ba, dan haka suka zama 'yan kallo, sai idan mazajensu sun saka su acikin shawarane.............✍🏼 *_Ya Rabbi ka gafarta iyayenmu😭👏🏻_* [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _________________________ _Happy marriage life *SANNA S MATAZU* ALLAH ya sanya alkairi da albarka a wannan aure, yabaku zaman lafiya na har Abadan da zuria d'ayyiba, bad'i muzo cin rangam💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻😄👌🏻._ __________________________ 👉🏻8⃣ .......Hidimar biki ta kankama gadan-gadan, dan har bak'in nesa sun fara isowa, a ranar alhamis aka gudanar da sister's and brother's day Wanda mune k'annensu muka shirya musu da yayinmu maza. da farko a tsakar gidan innaro aka shirya, saboda su Abba bazasu barmu mu saka kid'aba a gidanmu, gashi mun gayyato k'awayenmu ne, sai abokan su yaa Nasser danasu Anas. daga baya kuma sai muka canja shawara saboda samun wani fili damukayi can k'asan layinmu, filin a zagaye yake da katanga an saka gate. Tunda safe suka fara shirye-shiryen gyara wajen, kasancewar sai 4pm za'a fara, mudai makaranta muka tafi nida fauziyya da Munubiya, dan munada lectures, amma sauran duk k'in zuwa sukayi, barema su Siyama amare. Around 3pm muka dawo gida, yauma kam da alama wasu bak'in sun iso, dan gidan Yakuma cika da yara da 'Yar hayaniya. Mun tarrar innarmu tana d'akin abbanmu, dan haka mukayi wanka muka fara shirin tafiya wajen taron, ko abinci bamu nemaba, dagani har munubiya mun iya makeup, kasancewar mama Rabi'a tasakamu wajen koya muda Ayusher lokacin damuka gama secondary, a d'an tsakanin kafin fitowar results d'inmu, taga damuyi zaman banza gamma muje mukoya wata 'Yar sana'ar, tunda bamusan inda rayuwa zata kaimuba. Ko gama shiryawa bamuyiba Rahma tashigo kiranmu inji su Aunty Rahaima, dan mune zamu musu kwalliya. Mun tarar dasu duk sunyi wanka dama mu suke jira, zaman musu kwalliyar mukayi, ni nafarama Aunty Hauwa'u, yayinda Munubiya takema aunty Ramlah. Kiran Ayusher yashigo wayar munu...., ta d'aga tana fad'in “kin isone?”. Bansan mitace mataba daga can, naji tace, “kizo muna 6angaren su Aunty Ramlah”. Babu dad'ewa saiga Ayusher itama, ta gaggada su Aunty's d'in, sannan muma tabamu hannu muka gaggaisa cikina musabaha. “lah dear nifa harna fidda ran zakizo ALLAH”. Ayusher tace “kibari kawai, wancan jarabbaben ne yasakani aiki, tuwo mama tayi da rana, kinsan kuma bayaci shi, shinefa ya tsareni wai saina masa sakwara, harfa nayi shirin tahowa”. “uhm ai lamarin yaa marwan saishi, matarsa dai taga banu wlhy, shi anya ma yata6a budurwa kuwa?”. Dariya duk muka sanya a d'akin, aunty Hauwa'u tace, “ai marwan akwai miskilanci wlhy shima, nifa zan iya cewa mun ta6a magana dashi kuwa?”. Ayusher tace, “yo aunty ai wannan kowama haka yake masa, komu muka gaidashi sai yaso yake amsawa, kullum mama cikin masa fad'a take amma abanza wlhy?”. Nann dai hira Yakoma kan yaa Marwan da mutane masu muskilanci irinsa, Munubiya ce mai kareshi, (dama ita suna d'an d'asawa, nice dai kamar muna ganin hanjin juna dashi danma ina tsoronsa ). Kasan cewar mu uku ne sai kwalliyar tai sauri, dan danan muka kammala, nida munubiya mukayi tamu muma, simple makeup mukayi, amma komai iri d'aya, dama haka mukeyi, komai namu kullmun iri d'ayane. Munyi k'yau, 6angarenmu muka koma mukayi shiri cikin blue d'in skirt da pink d'in Riga kamar yanda aka tsara sai veil shima blue. Na jujjuya ina kallon kaina a mirror, “kai jama'a nikam bazan iya fita hakaba gaskiya”. Ayusher dake kwance tana danna wata tad'ago ta kalleni, “kai amma kuma wlhy kayan sun miki k'yau, kinganki kuwa? dan ALLAH ki barsu, kiyi rolling veil naki kawai”. “kai ba munaya kad'aibafa, nima bazan iyaba, after dress zan d'ora wlhy”. Dariya Ayusher tayi, ta tashi zaune tana ajiye wayar, “waiku miyasa k'auyawane sister's, naga a ke6antaccen waje za'ayi?”. “amma kuma dai ai akwai maza kema kin sani”. “to alaranmiya, Ku saka, amma kafin Ku saka d'in nidai kuzo miyi hotuna”. Gaskiya koni nasan munyi k'yau, kasancewar mud'in fararene, kalolin duk sai suka kar6i jikinmu blue & pink. Wanda bai saniba saiya ce mu 'yan uku ne har Ayusher, dan muna matuk'ar kama da juna, sai dai Ayusher tafimu haske da d'an jiki. Sai da mukad'anyi hotuna sannan muka fito. Innarmu tace kunyi k'yau, amma dan ALLAH kar inji wani yayi abinda za'ace gashi-gashi, Ku kama kanku da mutuncinku kunga dai acikin anguwane, idon kowa akanku yake”. Mukace to innarmu insha ALLAH. mun fita tana binmu da addu'a. A k'afa muka taka har wajen taron, tunkan mu k'arasa muke jiyo tashin kid'a. wajen dank'am yake da 'yanmata da samari, k'awayen amare da namu muma, sai 'yan uwa kuma da abokan su yaa Nasser, dama shi ya Hameed bai gayyaci kowaba, yace ya bar mana mu k'anne (shidama ba auren farko bane). Tunda muka shigo akai mana caa da idanu, wasu tsantsar kamarmu ce tajawo hankalinsu kanmu, wasukuma burgesu mukayi, wasu kuma gulmarmu sukeyi da zaginmu, to dama shi taro ya gaji hakan, ballemu da ake ganinmu k'ask'antattu agidanmu, kamar kowama yafimu komai. Amare suma duk sunyi k'yau cikin tasu shigar ta Riga da wando pink gaba d'aya, sai suka d'aure k'ugunsu da blue d'in belt, suka d'aura jacket blue. Snacks ne kawai akad'anci a wajen da drinks, sai pictures da'aka d'auka da video, 'yan mata sunata casar rawarsu da samari, mudai muna daga gefe zaune muna shan kallo. mun rarraba gifts d'in damuka tanada, bawani Abu bane masu tsada. silifas d'in wankane sai brush, MacLean, soson wanka da sabulu d'ad'd'aya aciki, gifts d'in nan mun shiryashine kawai dan tsokana dama. gabda magriba taro yatashi lfy, kowa ya kama gabansa. muma gida muka koma. ★★★★★ Washe garima saida mukaje makaranta, sai dai 11:30 muka fito lecture, ALLAH ya taimakemu muka samu taxi da wuri. Sanda muka dawo har 'yan jere sun dawo, kowa dangin mamarsa sukaje jerensa, shiyyasa mukaji tsitt babu gutsiri tsoma. Muna dawowa ko wanka bamu tsaya yiba mukaci abinci muka tafi shagon auntynmu data koyar damu makeup domin yin k'unshi da saloons. Cikin farin ciki ta tarbemu, dan mun rabu da ita cikin mutunci bayan mun iya aiki, Aunty salamah batada damuwa, inkaga tana maka fad'a to baka fahimtar abinda take koyar dakai ne, kwazon damuka nuna alokacin yasa takeji damu over. Tana kiranmu 'yan ukun ta. K'unshi aka mana mai k'yau da gyaran kai, (dan d'aurema k'arya gindi irinnan aunty salamah harda mana gyaran jiki😊, wai tanaso muma musamo mazajen aure🙈). Kowa ya gammu yasan munyi k'yau sosai. Amakare mukaje gida, dan mun tarar amare nata jiranmu mu musu kwalliya, 'yan gidanmu harsun fara k'ananun magana, wai wulak'ancine yasa muka fita ai, kuma muna kallon lokaci yana k'urewa mukak'i dawowa. hakan da innarmu taji yasata kiranmu tana mana fad'a, hak'uri muka bata dacewa gamunan a hanya. Masifa mukaitayi nida Ayusher, munubiya na bamu hak'uri, wlhy badan innarmu ba da bazanyi kwalliyar nanba yau. Babu zancen mu huta muka hau musu kwalliyar. aikam ranar k'in fita wajen kamun nayi da akayi a tsakar gidanmu, kwanciyata nayi, innarmu taitamin fad'a kuwa.😕 Washe garin asabar d'aurin aure, dakam gidanmu yacika tab, 6angarenmu dai da sauk'in mutane, sai mama Rabi'a kawai da matan abokan Abbanmu. K'arfe goma aka d'auro auren yaa Hameed da amaryarsa, sai yaa Nasser shima da yaa Shafi'u. Na 'yan matan kuwa sai k'arfe 1:30pm. K'ofar gidanmu yacika dank'am da jama'a ta ko'ina, 'yan siyasa tawagar senator halliru da abokan su Sa'eed, hakama mijin aunty Rahaima d'an siyasane, dan haka harda governor a mahalarta taron d'aurin auren. Har aka gama d'aura aurarrakin ina d'akinmu kwance, ko wanka banyiba, garama munubiya da Feena da Ayusher su duk sunyi, amma suna d'akin basu fitaba, sai balkisu k'awarmu da itama tazo mana. Hira suketayi, nikam dai ina kwance kaina namin ciwo. Gidanmu babu masaka tsinke, tako ina jama'ane, amare ansha k'yau, su siyama baki har k'anne an auri 'ya'yan sanata, hakama iyayensu sai burga sukeyi, ranar munga gasar dressing wajen iyayenmu mata kam, kowacce so take ace itace uwar amarya datafi kowa fita. Innarmu kam babu ruwanta, shiga d'aya tayi ta atanfar da Abbanmu yamusu Na fitar biki, sai da yamma ta canja da less. Aranar kowaccensu tayi yini. Baza'a kai amareba sai washe gari, saboda anason agudanar da dinner waje d'aya, amma an kawo nasu yaa Shafi'u sudai. Yau d'inma dai mune muka musu kwalliyar su dukansu, kafin k'arfe 8pm afara kwasar mutane zuwa wajen daza'a gudanar da dinner d'in. Gurin yayi k'yau sosai, yayinda aka shirya ma amare da anguna hi table. Sai dai kuma wata sabuwa, ba duk angunan bane suka halarci wajen dinner d'in, nan fa aka fara 'yan gulmace-gulmace tsakanin dangin iyayenmu mata, tuni labari harya kai kunnuwan iyayenmu mata dasuke zaune a gida. Amaren da babu angunansu sunsha kuka, wad'anda kuma dama sukasan angunan nasu ustazaine bazasu zoba basu damuba. Haka dai aka gudanar da dinner d'in zukatan wasu babu dad'i, tunkan agama ma wasu sukaita tafiya gida abinsu. K'arfe 11 aka tashi. A wajen dinner kam nayo saurayi mai suna Fu'aad, hakama munubiya da Ayusher dun sunyi, Fu'aad k'yak'yk'yawa dashi masha ALLAH, duk da dai bawani sake masa nayiba ya burgeni. Su Ayusher sunata tsokanata, nidai ban kula suba. Washe gari da safe kuwa saida abin yazama fad'a, wai ankama wasu suna gulma akan rashin zuwan sauran anguna, kuma dangin momy Hadiza ne, aikam sosai aka zuba rikici, har saida abbanmu ya tsawatar. Aranar aka shirya kai amare, dole sai dai a rarrabu, tun la'asar aka fara kawo motoci, baba k'aramine yabada shawarar ahad'a tafiyar kawai gaba d'aya, su aunty Hauwa'u suma su siyama rakiya, sannan suma haka. Haka kuwa yayima wasu iyayenmu mata dad'i, dan kobabu komai saji yanda gidan kowacce ya kasance. mun fara kai su Siyama da Zarah, wad'anda babu alamun kuka a idanunsu, gidajensu jere da juna, sunyi k'yau masha ALLAH, kayan gado dai duksu Abba sukayi, kuma kud'insu d'aya, saidai kowa da za6insa, kayan kitchen ne kowa uwarsa tayi da sauran tarkace, ananne kowa ya ware ido dan aga kwazon uwar mutum, nidai agareni babu makusa, gidansu Zarah duk yayi. Mun ajiyesu tareda k'awayensu, mukuma muka tafi kai sauran. Daga Nan sai gidan aunty Rahaima, itama masha ALLAHU wlhy, saidai mak'iyi, gidanta yayi k'yau, sai dai tanada kishiya. Saikuma gidan aunty khaleesa, itama dai d'in zamm zamm wlhy, daga nan sai aunty Ramlah, wlhy itama yayi d'as, itama tanada kishiya. Aunty Hauwa'u ce k'arshe dan itace babba, itama gidanta yayi k'yau sosai. Nidai aganina babu wadda mahaifiyarta batayi k'ok'ari ba wlhy, amma hakan bai hana sauran gumtso gulmarmakiba aka taho da ita. Kasancewar duk babu Inda muka zauna aka taho gida da wuri, harzamu wuce Fu'aad daya d'akkomu yace bari yashiga Birnin gayu plaza damu. Nace a'a muwuce gida kawai, kar aga kowa yadawo mu bandamu, gashi lokacin har 8:30pm ya wuce. Ayusher ce tace indai bazamu dad'eba ashiga, saimuce muna gidajen su siyama mu, mun zauna jiran anguna. Kamar dai nace a'a amma nayi shiru, saboda naji munubiya da feena suma sun bada goyon bayan mu Shiga, sannan Fu'aad yace bazamu dad'eba. Ya kalleni murya k'asa-k'asa yace, “ginbiya bakice komaiba?”. Murya a sanyaye nace, “indai bazamu wuce 1hour ba muje”. “insha ALLAHU my luv bazama mu kaiba”. A kasalance Na d'aga masa kai saboda agajiye make ti6is. Haka yashiga wajen nidai zuciyata Na dukan uku-uku daban San Na miyeba. Munshiga cikin plaza d'in, bansan takamaimai miyasa Fu'aad yace mushigo wajenba, tunda dai bawani abin ci ake saidawa a wajenba. Mun shiga 6angaren kayan kwalliya, yace kowa yaza6i abinda yakeso. Nidai nace masa a'a mun Gode. 6ata fuska yayi yana hararata, ya maida kallonsa gasu munubiya dake tsaye “please dan ALLAH karku biye mata, kuje Ku d'auka”. Badan suma sunasoba suka amsa da to. Ya kalleni yana fad'in “mujeto ni na d'ebar miki”. bance masa komaiba nabi bayansa ganin kamar yayi fushi, wayarsa aka kira, ya zaro daga aljihu, saida yad'an saci kallona yaga hankalina baya kansa sannan ya d'aga, murya k'asa-k'asa tamkar mai gulma yace, “nagama aikina”. Dawowa yayi wajena bayan ya katse wayar, da kansa yake za6ar mini duk abinda yadace. Su munubiya ma sunacan suna d'auka, kamar ance munubiya ta bar wajen saita zagaya tabaya, a dai-dai wannan lokacinne shikuma yake tunkarowa shida wasu matasan samari guda biyu, da alama yana zagayene kowani abun daban. tafiya yake cikeda nutsuwa da sarauta, sai sautin takunsa dakakeji, tunkan su iso gareta k'amshin turarensa ya iso. Waige-waige munubiya tafara, tanason tuno mai wannan k'amshin. bata ankaraba saijinta tayi tatafi suuuu santsi ya kwasheta. Shi mutumne mai yawan tausayi da taimako, da sauri yayo kanta kafin taje k'asan, Dan yasan fad'uwarta a wajen babban had'arine, yakai hannu zai rik'eta itakuma ALLAH yabata ikon dafe wasu tarin baskets dake wajen. Cikin runtse ido da sauke ajiyar zuciya ta furta “Alhmdllh”. Janyewa yayi daga rankwatowar dayay kanta tamkar zai rungumeta, batareda yace uffanba yafar wajen. Muduka akan idonmu komai ya faru, wad'anda suke tare dashine sukaima munubiya sannu, mukuma muka k'araso da sauri gareta muna tanbayarta babudai wata damuwa ko?. “babu komai Alhmdllh”. ‘tafad'a tana gyara tsayuwarta’. Nace, “kunga kuzo mu tafi hakanan, wlhy inajin tsoron agane bama gidansu siyama”. Duk suka amsa da gsky mu tafi, da k'yar muka yarda mukaje wajen biyan kud'in. yabiya sannan muka tafi. ALLAH ya taimakemu ba'a mana fad'aba. Duk cikinmu babu Wanda yakuma maida hankali akan abinda yafaru a birnin gayu plaza, saidai abin yakasa barin raina, kamar zuciyata tana cikin fargaba, amma bansan ta miyeba, ita kanta Munubiya wani sukuku nake ganinta, bandai tanbayeta ba Na share. Washe gari Monday, muka tashi da shirin makaranta, saida muka gama gyara gidan tsaf sannan muka tafi harsu Ayusher, dayake lectures d'inmu Na yau sai 1:30pm ne. yauma sauran 'yan uwanmu bakowa yaje school d'inba ma har fauziyya. Tun muna tsaye abakin titi muna jiran taxi naga wasu tsirarun mutane nabinmu da kallo. ban kawo komai arainaba muka samu taxi. Driver ma yana tuk'i yana kallonmu ta madubi, sainaga kuma ya kalli takardar dake saman cinyarsa. d'an fara tsarguwa nayi, amma saina dake ina zaton irin dirobobin nanne masu shegen kallon tsiya. Da muka sauka cikin makaranta ma bata sauya zaniba, kallonmu akeyi har ana nunamu, wasu da jaridu a hannu wasu kuma waya. Munubiya tace, “Manaya bakiga abinda ke faruwaba tundaga fitowarmu gida zuwa nan ne?”. “nagani wlhy Munubiya, bansan miyakawo wannan kallon k'urilla d'inba, dama bakiga kallon da direban can yake manaba ni da ke harya saukemu, ko sanda muke sallama dasu Ayusher idonsa Na kanmu kyam kuma yana kallon wata jarida dake cinyarsa”. Muduka kallon jikin junanmu mukeyi, babu wanda shigarsa tazama aibu acikinmu, sannan bama tareda wani abin kallo, Hannun juna muka kama muka cigaba da tafiya cikin tsantseni da nazartar kallonda 'yan uwanmu d'alibai suke mana. Tunda muka shigo cikin class sai duk aka zubo mana idanu, kuma anata k'us-k'us. yanzu kam hankalinmu yatashi sosai, wai mike faruwane? saikace yau mutane suka fara ganinmu? shin yaune muka fara shigowa makaranta?. Bamu da mai bamu amsar tanbayarmu, muka nufi Bilkisu dake zaune itama tazubo mana idanu, ga jarida agabanta, kamar yanda muka gani wajen sauran 'yan department d'inmu, wasu narik'e da jaridu wasu wayoyi, sunyi group group kuma suna k'us-k'us. Da sauri Na k'arasa zan d'auki jaridar gaban Bilkisu amma saitayi saurin d'aukewa............✍🏼 Babbar magana, shin mike faruwane? kallonmi jama'a kema su Munubiya? Sannan mi ake kallo a jikin jaridar da wayoyin kuma?🤦🏻‍♀. Nasan masu karatu ma wannan amsar suke son sani🤔 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻9⃣ .......K'yaleta nayi najuya sit d'in bayanmu Na fusge ta hannun wani guy, rubutun farko dage jikin jaridar a shafin farko na tsirama idanu. *_BABBAR MAGANA, GALADIMA SAMEER RUNGUME DA MATASHIYAR BUDURWA A PLAZA 'DINSA SUNA SUMBATAR JUNA!!_* sai kuma hoton dake k'asan rubutun shima har kala biyu, Na farko abinda yafarune na fad'uwar Munubiya a birnin gayu plaza, har Galadima yay yink'urin taimakonta amma tadafe baskets ko ta6ata ma baikai gayiba, amma abin mamaki da al'ajabi a hoton galadima ya rungume munubiya ne bakinsa akan nata. Hoto nabiyu kuma ni da shi ne afilin idi lokacin damukayi karo har wayarsa ta fad'i, ko kad'an bai ta6aniba, ko waya daya kar6a a hannuna hannuna danashi basu had'uba, amma anan an nuna hoton yana rik'e da hannuna duka biyu muna kallon juna. “Innalillahi” nafara maimaita jikina har yana rawa, gawata uwar jufa data fara jik'a sassan jikina, lallai dolene duk inda muka gitta abimu da kallo. Ju yowa nayi na kallo munubiya dake tsaye a bayana, itakam hawayema takeyi. Jikina a sanyaye nakama hannuta muka fita daga cikin hall d'in, kallon da ake Manama ayanzu yafi na d'azun, Dan labarin sai kuma yad'uwa yakeyi yanzun. Muna fitowa muka samu taxi sai gida. Tunda muka sauka naga wasu gungun samarin dake layinmu a majalissarsu sun zubo mana idanu gaba d'aya, tuni zuciyata tafara tsitstsinkewa, kenan labarin harya iso nan?. Dagani har Munubiya jamukai muka tsaya, saboda ganin dukkan ahalin gidanmu tsaye cirko-cirko a tsakar gida, hardasu yaa hameed anguna, ga bak'i dabasu gama tafiyaba, innarmu kwance akan tabarma maman fauziyya namata fifita, ga Abbanmu kusada ita tsugunne yana shafa mata ruwa. Jaridar dake hannun baba k'arami mukabi da kallo, bansan sanda wani kuka yatahominba nima, sa6anin da munubiya kawai keyin kukan. Da gudu mukayi kan innarmu, amma sai yaa hameed ya daka mana tsawa, “karku sake Ku ta6ata wlhy, idan bahakaba jikinku kuwa saiya fad'a muku”. Babu shiri mukaja burki, amma sai muka durk'ushe ak'asa muka fashe da kuka. Innro tace, “kwayi kuka kuwa munafukai, ahiyyasa ai ANNABI yace a auri mace tagari, Dan 'ya'ya susami uwa tagari, yo wannan aimu ba sabon abu baneba agaremu, tunda dama halin uwarku kenan, itama saida tagama tambad'arta a titi aka k'ak'abama d'ana”. Rintse idanu nayi saboda yanda maganganun innaro ke sukar zuciyata. Dady yakatseta da fad'in “dan ALLAH inna kiyi hak'uri kibar maganarnan”. “hameesu barni nafad'i gaskiya, wannan abin kunya har ina, wai jikokinane yau aka buga ajikin jarida namiji rungume da d'ayarsu a titi” ta face hanci tana share hawaye da bakin zani, “ALLAH ya wadaran irin wannan rayuwa taku kuda uwarku, kun jawo mana abunkunya, yanzu dawane ido duniya zata cigaba da kallonmu” feeet, takuma fyace majina”. Mudai ni da munubiya muna durk'ushe rungume da juna Luna rairai kuka maiban tausayi dacin zuciya, yayinda 'yan gidanmu da sauran 'yan biki suketa k'us-k'us a tsakaninsu. Isowar likita yasa aka kama innarmu aka maida falon Abba, a sank'ame take tamkar gawa.... ★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★ *_GAGARA BADAU PLACE_* Shirye-shiryen komawa India yakeyi hankalinsa kwance, Dan yau zai koma ga mahaifansa da 'yan uwansa dake can, jirgin k'arfe 8pm zaibi. Yana gama had'a 'yan abubuwan dazai iya buk'ata yadawo falo ya zauna, sanye yake cikin farare k'al d'in kayan Adidas na training, dogon wando da Riga mai dogon hannu, yasaki hular abaya, kayan sun masa k'yau sosai. Kallo d'aya yayma abincin dake kan center table d'in ya d'auke kansa, cikin k'asaitacciyar muryarsa mai cikeda isar masu mulki naji ya furta “Saykin k'ofa”. Kai kace anmasa dolene saiyayi maganar. Da hanzari sarkin k'ofa yashigo falon, ya zube a k'asa “barka da hutawa ya shugabana”. Kansa kawai ya jinjina, sannan yace, “waye yakawo abinci nan ne?”. “ya shugabana bansan daga ainahin wane 6angare bane, amma bayin dasuka kawo daga 6angaren sarauniya Zulfah ne”. Baice komaiba ya d'aga masa hannu alamun yatafi. Sai da yad'an rissinar da kansa alamar girmamawa sannan yamik'e, dokace agareshi shi bayason kirarin da akema 'yan gidan sarautar. dan haka basa yimasa shi, Saboda gudun 6acin ransa. zamewa yayi yay kwanciyarsa akan doguwar kujerar ya lumshe idanunsa batareda yabi takan abincinba. Sallamar sarkin k'ofa tasakashi bud'e idanunsa akansa, ya amsa sallamar bisa la66ansa, sarkin k'ofa yazube agabansa, cikeda girmamawa yace, “ya shugabana yalla6ai Muftahu yace amasa iso gareka”. Alama yamasa akan yabada izinin ya shigo. Fita sarkin k'ofa yayi. babu dad'ewa saiga Muftahu yashigo da sallama, Galadima yabud'e idonsa yana kallonsa tareda amsawa. Zama yayi kujerar dake kallon Galadima, yace, “yalla6ai barka da hantsi”. Murmushi Galadima yayi, ya tashi zaune sosai yana fad'in “my man daga ina haka naganka ayikice? bakaje aikibane?”. Ajiyar zuciya Muftahu ya sauke, yacije le6ensa na k'asa yana mik'ama Galadima jaridar dake hannunasa, “nafita wlhy sainaci karo da wannan jaridar data fito a safiyar yau”. Cikin halin ko inkula Galadima yace, “Miye had'ina da jayidan to?”. “Kayi hak'uri ka kar6a ka duba”. A shafin farko yay karo da abinda yasakashi sake kallon Muftahu, kai Muftahu ya d'aga masa alamar yacigaba. *_ANYI WALK'IYA...., GALADIMA DA AIKA-AIKA A FILIN IDI_* cikin hanzari yabud'e shafin farko, nankuma an saka. *_BABBAR MAGANA, GALADIMA SAMEER RUNGUME DA MATASHIYAR BUDURWA A PLAZA 'DINSA SUNA SUMBATAR JUNA!!_* sai hoton farko dana biyu, wad'anda suka d'aure kansa, danshi gaba d'ayama ya manta daduk abinda yafaru, tundaga na birnin gayu plaza harna filin idi d'in. d'agowa yay yakalli Muftahu sannan ya maida kallonsa ga dogon rubutun da akai akan sharhin hotunan. bazai iya karanta rubutun ahakaba, saiya fara waige-waigen neman medical glasses d'insa. Fahimtar haka da Muftahu yayi yace, “ina yake in d'auka maka?”. Da hannu ya nuna bedroom d'insa ba tare da yace komai ba. Mik'ewa Muftahu yayi yanufi bedroom d'in, babu dad'ewa saigashi yadawo, ya mik'a masa sannan yakoma inda yake da ya zauna yana fad'in “ko ka kawo na karanta maka”. Nanma baice uffanba yamik'a masa jaridar, kansa ya maida jikin kujerar ya jingina ya lumshe idanunsa. Tiryan-tiryan Muftahu yafara karanto k'aryar da aka jera jikin jaridar, ko sau d'aya bai motsaba, amma yana saurarensa. Muftahu yagama cikin sauke ajiyar zuciya, Amma tabbas wannan wata k'ullaliyace, ai ba abinda yafaru kenanba jiya a birnin gayu, ni nama rasa mizan cema wannan gidan jaridar wlhy”. Galadima ya bud'e idonsa dake a lumshe, ya kad'a yay jajur saboda 6acin rai, akan Muftahu ya saukesu batareda yace komaiba, tuno abinda yafaru a filin idi yayi kusan sati 4 kenan, tabbas sunyi karo da yarinya, wadda ayanzu haka ko fuskarta bazai iya tunawaba, dan ko'a waccan ranar kallo d'aya yamata, a jiya kuma ko ta6a yarinyar baiyiba ALLAH ya kareta daga fad'uwar dazatayi. jinjina kansa yayi cikeda 6acin rai da mamaki. Muryarsa a sark'e yace, “Muftahu imason bayanai akan yayannan najikin jayiday su duka”. “ok yalla6ai, amma ai yarinya d'ayace duba kagani”. Kar6ar jaridar yayi yakuma kallon hotunan, tabbas duk yarinya d'ayace, wannan ya sake tabbatar masa da an shirya masa hakanne. Mik'ewa yayi yazari mukullin mota batareda yace ma Muftahu komaiba, ganin haka shima Muftahu saiya mik'e yabi bayansa. Cikin sauri dogaren dake binsa inhar zai fita suka taso gareshi, amma saiya d'aga musu hannu. yana k'ok'arin bud'e motarne Jakadiyya ta iso inda yake... Cikin rissinawa tace, “barka da hantsi galadima”. Bai iya amsa mataba, sai hannu daya d'aga mata kawai. Kuma rissinawa tayi tace, “Galadima takawane yabani izinin in kirayeka”. Kallonta yayi zaiyi magana saikuma yay shiru ya maida motar yarufe tareda cillama Muftahu dake bayansa kyes d'in. Muftahu ya cafe. Komawa yayi 6angarensa yashiga wanka, kusan mintina 40 sannan yafito sanye da bathrobe fara k'al, bai wani d'au dogon lokaciba yay shiri cikin k'ananun kaya, yayi k'yau sosai, ya feshe jikinsa da turarensa masu matuk'ar k'amshi. Wayarsa ce tashiga ringing, baibi takantaba yacigaba da hidimarsa, dama tun yana bathroom yakejin ana kiransa. ta baya yabi inda bayi bazasu isheshi da gaisuwa gaisuwa d'innanba, dayake sarki yana gida, yau ana hutun zaman fada saboda tunawa da abinda yafaru da tsohon sarki (mahaifin Galadima Sameer) duk ranar litinin tana zama ranar daba'a zaman fadane... ★.★.★.★.★.★.★.★.★.★ Kowa ya ganmu yasan muna cikin rud'ani, da k'yar aka samu innarmu ta farfad'o, sai dai an hanamu mushiga mu ganta. Gidanmu kam abin nema yasamu, hakama cikin anguwa, saboda yad'uwar labarin a social Media. Muna zaune a falo duk mun zabga uban tagumi dagani har munubiya, idanunmu duksun kunbura saboda kuka, Ni ba abinda yafaru a jaridar ne yafi damunaba, halin da mahaifiyarmu ke ciki shine babbar matsalata, bamuda kamarta duk duniya, bazanso wani Abu ya sameta asanadinmu ba, bayan bak'incikin datake k'unsa agidanmu kuma. Kamar anjeho mama Rabi'a itada ya Marwan suka shigo falon. mun tsorata kwarai da gaske, cikin daka tsawa mama Rabi'a take tambayarmu innarmu. Hakanne ya tabbatar mana da suma labarin yaje musu. munubiya ce tabata amsa cikin kuka, sannan tace “wlhy mama sharrine, ba abinda yafaruba kenan n......”. Saukar marin datajine yasakata rufe bakinta 6am, kafin na tantance mai Marin nima naji saukar nawa. Ko kad'an yaa Marwan baiji tausayinmu ba, saida yamana lik'is da duka, dak'yar Dady ya kar6emu a hannunsa, amma baba k'arami da Abbanmu casukai yama k'ara mana. 'Yan gidanmu duk sunfito cirko-cirko a tsakar gida, kowa na tofa albarkacin bakinsa, gashi akwai sauran 'yan biki dabasu gama tafiyaba. Iyayenmu da yayinmu duksun taru akanmu, ana tambayarmu wacece daga cikinmu. Kafin Munubiya tayi magana nayi saurin cewa “kuyi hak'uri iyayena, nice munaya a gaba d'aya hotunan, wlhy kuma tsautsayine, amma ba ainahin abinda yafaruba kenan”. Munubiya zatayi magana nayi sarin rik'e hannunta alamar kartace komai, “karki d'aurama kanki abinda ba laifinkiba Munubiya, nice Munaya na aikata....” Itama cikin kuka tace “wlhy bake baceba, nice, wlhy nice”. Nima nace “wlhy nice”.. .... Tsawa Abbanmu yadaka mana, atare mukayi shiru yace “nasan dama Munaya kece, Munubiya bazata aikata wad'annan abubuwan ba, dukda kema d'in nayarda da tarbiyyar dana baki, amma bansan miya kaiki ga aikata hakanba, shiyyasa ranar idi mukaita nemanki, Ashe kinacan kina d'akko mana magana, tunda aure kikeso zan miki, nabaki nanda sati 2 kacal, inbaki kawomin mijiba zan had'aki dadu Wanda nayi niya”. Yana gama fad'ar haka yatashi ya fice, baba k'arami ma ficewarsa yayi. Wani kuka mai tsuma rai muka kuma fashewa da shi, musamman ma ni danasan nasaka kaina a tarko, amma hakan shine dai-dai, bazan amince naga 'Yar uwata cikin bak'in cikiba, insha ALLAH koma minene zan jureshi, muniya tanada hak'urin dazai iya cutar da ita akan wannan lamarin, gashi baba yafurta in ban fiddo da mijiba zai auramin Wanda yaso, to idan hakan ta kasance kan Munubiya wane hali kuke tunanin zata shiga? Musamna dabamusan gidan dazamu iya fad'awaba tunda nasan abinda Abba yafad'a tabbataccene, dan shi baya magana biyu. Dady ne yashiga lallashinmu, tareda mana nasiha da nuna mana illar abinda muka aikata, musaman ma ni. ya Marwan kam sai antayamin harara yakeyi shida yaa hameed. Yinin yau kam kuka muncishi harmun godema ALLAH, mu duka kwance muke rijif da zazza6i, har akayi isha'i bamu kumajin motsin kowaba, mukuma muna d'aki kwance mu duka k'udundune a bargo. Su Aryaan sunacan nanuk'e da innarmu dake 6angaren Abbanmu har yanzun, dan haka 6angarenmu saiya kasance tsitt. a ranar dai haka muka kwana babu lafiya nida Munubiya, babu mai iya taimakon wani acikinmu, ga yunwa ga damuwa ga ciwo. Zuwa asubahi ko salla kasa gashi muyita mukayi, dan k'arfinmu yagama k'arewa...😭 ★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★ Ya isa sassan mai martaba, bayan masu tsaron k'ofa sun gama kwasar gaisuwa suka masa iso. Izinin shiga mai martaba yabashi. Falone k'aton gaske, Wanda nikaina banmasan yanda zan musalta k'yansa da girmansaba, ga kujeru rukuni-rukuni, ko ina yagama d'umamewa da sanyin AC, gawani k'amshi na musamman. daga can gefe na hango mai martaba kishingid'e bisa wani lallausan carpet da aka k'awata da tarin tum-tum, gabansa tirene dake d'auke da jug na glass cikeda zo6o, sai wani k'aramin kwano na tangaram Wanda bansan miye acikiba, saikuma k'aramar butar shayi awani tiren daban, da mug guda d'aya. Fuskarsa d'aure take tamau alamar yana cikin 6acin rai, ga jarida a hannunsa. Cikeda girmamawa Galadima ya zauna a gefen dardumar, ya tankwashe k'afafunsa sannan ya risina yana fad'in “barka da rana ranka ya dad'e”. Mai martaba bai amsaba, sai ma cilla masa jaridar hannunsa dayayi. Galadima yabi jaridar da kallo batareda ya d'aukaba. “ka d'auka ka duba mana, dan inason sanin gaskiyar zancen”. Kan galadima a k'asa yace, “takawa nima yanzu Muftahu yakawo min nagani, nama fito zanje ga gidan jayidayne kiyanka ya isomin, amma wlhy Abba ba gaskiya baneba, ka.......” Da sauri mai martaba ya d'aga masa hannu cikin 6acin rai “mi kakeson fad'amin? kana nufin zasu buga abinda baka aikata bane? ai sunsan gidan daka fito, haka kawai bazasu maka sharri ba kodan gudun abinda zaije ya dawo. Sameer yanzun nan da mutuncinmu kaje ka aikata wannan son zuciyar domin ka 6atama wannan masarautar suna? Lallai kacika d'an halak, kuma kayi dai-dai, tabbas ka kafa tarihin dawani bai ta6a yin irinsaba a wannan masarautar, Dama Ashe kabud'e waccan plaza d'inne domin son zuciyarka? Yanzu da ace lafiyar Yaya k'alau wane irin hali kake tunanin zai tsinci kansa? Ina ganinka shiru-shiru Ashe kaid'in shaid'anine”. Runtse idanu Galadima yayi zuciyarsa na k'una da kalaman mai martaba k'anin mahaifin nasa, amma yagaza furta komai, sai idanunsa daketa k'are rinewa zuwa jajazur. Har mai martaba yak'araci fad'ansa yagama Galadima bai iya furta komaiba, kansa ak'asa ko motsi baiyiba. “katashi kabani waje, k'arfe 8:30pm akwai meeting, saika jira hukunci daga mama Fulani ”. Rissinar da kai Galadima yayi yace, “ALLAH ya huci zuciyayka, na bayka lafiya”. Banza mai martaba yay masa, yatashi yafice shikuma cikin k'unar zuciya. Yana fita wayarsa ta fara ringing, ransa adagule yacirota da nufin kashewa gaba d'aya, saiyaga *_My dear Momma_* rintse idanunsa yayi ransa nakuma suya, yasan tabbas labari ya Isa gareta kenan, wannan wace irin masiface, mahaifiyarsa dake wata k'asa har ankirata an Sanar mata, ko halin datake ciki baza'a kallaba?. Kasa d'aga wayar yayi harta tsinke. Tabbas duk Wanda yake gidan jaridarnan saiyayi Dana sanin saninsa arayuwa. Kiran Momma ne yakuma shigowa, yanzuma bai d'agaba harya k'arasa sashinsa. Sai da ya zauna sannan yafara k'ok'arin nemanta cikin suyar zuciya data ruhi...............✍🏼 To masu karatu, ko wanene da wannan aika-aikar? tabbas yau Munaya tabani matuk'ar tausayi daga ita har munubiya, kai harma Galadima.🤦🏻‍♀ Kumuje zuwa danjin Yaya kuma zata kasance🙆🏻?. Yanzufa aka fara wasan👌🏻⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀🤾🏻‍♀ *_YA ALLAH ka gafartama iyayenmu😭👏🏻_* [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻🔟 .......Maman Fauziyya ce taga shirun yayi yawa narashin gittawarmu ta aiko Kamal yagani muna nan, dan ita azatonta ko mama Rabi'a tawuce damu gidanta ne. Da gudu yakoma ya sanar mata gamucan babu lafiya a d'akinmu. ai bata tsaya jin k'arshen zancenba ta garzayo, halin data iskemu aciki itama hankalinta yakai k'ololuwar tashi, takira baba k'arami a waya tana Sanar masa, duk da haushinmu dayakeji hakan bai hanashi shiga tashin hankaliba shima. atare suka shigo da dady, shima abbanmu sai gashi yashigo. Duk kuma jikinsu sai yayi sanyi, aganinsu yakamata su sauraremu ajiyan, amma duk da haka babu iyayen dazasuga wannan abun hankalinsu bai tsashiba, garashi d'an manyan mutanene, nashi mai sauk'ine, amma mune awahale. Haka aka kira doctor yaduba mu, yace damuwace ta haddasa mana zazza6in, sai kuma yunwa. Da k'yar maman fauziyya ta taimaka mana mukayi wanka da ruwa mai d'umi, sannan mukayi sallar asubahi. tea ma dak'yar muka shashi sannan mukasha magani, still kwanciya muka k'arayi, nan barci ya kwashemu. Dadyne ya kalli 'yan uwansa, cikin damuwa yace, “yaya Auwal yanzu bazamuyi wani yunk'urin bincike akan lamarinnan ba? ni dai sainake ganin kamar yarannan bazasu aikata hakaba, tsawon shekaru muna tare dasu, bamu ta6a jin makamancin abinan ba daga garesu, sainake ganin bai kamata mu yanke hunci ba akan abinda bamuda tabbas kuma cikin fushi”. “Hameesu karka goyi bayansu akan wannan lamarin, babu yanda za'ayi abuga labarinan alhalin bai faruba, kaduba fa shi yaron d'ane ga Sarki, shinema Galadima, kodan tsoron abinda zaije yadawo ai nasan gidan jaridarnan saji tsoron buga labarin”. “hakane yaya, amma baka ganin mak'iyanshi zasu iya amfani da wannan damar domin 6ata sunansa? maybe kuma su yaranmu tsautsayine ya gitta akansu”. “maganarka gaskiyane Jafaru, nima wlhy hakan nake tunani, amma yakamata mujira muji daga gidan Sarki, Dan inhar Dan 6ata sunan yaron akayi nasan bazasu k'yaleba, kuma zasu nememu”. Ajiyar zuciya Abba ya sauke yace, “nidai koma minene gsky aure yakamata ayima Munaya, Dan nikam banta6a cin karo da abinda ya rud'ar daniba irin wannan, mahaifiyar yarannan wlhy batayi barciba jiya, kwana tayi kuka, kuna ganin dai irin cin zarafin da inna tadinga mata jiya a tsakar gida gaban kowa, shin minene laifin A'isha akan wannan lamarin? zata aiki su Munubiya ne akan suje su aikata hakan?”. “kayi hak'uri yaya, lamarin inna sai hak'uri, kasan dai halinta ai”. Haka sukaita tattauna yanda zasu 6ulloma lamarin. ★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★ Jiki a sanyaye ya danna kiran Momma, bugu biyu ta d'aga, cikin girmamawa ya gaidata, ta amsa itama cikeda kulawa kamar yanda ta saba. hakanne yad'an sakashi jin sanyi a zuciya, ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in “Momma ya jikin Abie?”. “Alhmdllh Moh'd. wani mummunan labari yanzu Ummu Erfaan takirani take sanarmin?, sai kuma ga mama Fulani ma takira tanata fad'a. yanzu kuma Sauban ya nunamin wasu pictures wai an turo masane”. Rintse idanunsa yayi cikin k'unar zuciya, murya a sark'e yace, “Momma nima haka kawai nagani”. “ban gane kaima haka kaganiba Moh'd, kagayamin gaskiya please, wannan ba k'aramin Abu bane bafa”. Da k'arfi ya cije lips d'insa tamkar zai hudashi da hak'ori, cikin wata murya dake nuna k'ololuwar 6acin ransa yace, “Momma wlhy bansan komaiba, yanay idi tabbas munyi kayo da wata yayinya hay wayata tafad'i ta fashe, jiya kuma yayinya takusan fad'uwa a plaza nayi yink'uyin taimakon ta saima ALLAH yasa bata fad'iba, kuma ko ta6a banyiba, shine kawai yau gidan jayiday nan suka maida pictures d'in haka fa”. Ajiyar zuciya Momma ta sauke, (dan tarigada tasan halin d'an NATA, duk da ba'a shaidar d'an yau musamman idan yabar gaban idonka) “Muh'd tabbas wannan k'ulline, amma kuma yarinya d'ayace ai”. “haka nagani nima Momma”. “yanzu mi sarki yace?”. “Momma wlhy maganay babu dad'inji, hayma sun shiyya meeting a kaina”. “Humm Muh'd wannan maganace mai girma, kuma tabbas domin 6ata sunanka ne da namu akayi, akwai kuma dalilinsu nayin hakan, ita wannan yarinyar kodai da saninta kokuma an shigo da itane saboda cikar manufarsu”. “Momma su waye to?”. “Masusan ganin bayanmu mana, sun biyo wannan hanyarne domin dak'ileka da ragema kaifi”. Wani naushi ya kaima k'aramin teble d'in gabansa na glass, nan take ya tarwatse. bai damu da ciwon dayajiba, cikin k'araji yace, “tabbas kafin suga bayana nizanga nasu!!! rayuwar mahaifina bazata salwanta abanzaba!! Saina wulak'anta dukkan masu hannu aciki kosu waye su wlhy billahi Momma! numfashina fansa akan mahaifina!!”. Dole Momma tacire wayar daga kunnenta saboda yanda Galadima ke magana cikin matsananciyar tsawa. Saman kujera ya wurga wayar, batareda ya katse kiranba, afusace yafito daga 6angaren nasa, tsawa ya dakama dogaransa. Gaba d'ayansu cikin rawar jiki suka nufi motocin da ke fake a wajen, ko jira abud'e masa baiyiba yabud'e yashiga. Hankalinsu a tashe yake daganin yanayin shugaban nasu, sunsan tabbas ran 'yan maza ya 6aci yau, Dan kowa yasan rashin son hayaniya irinta Galadima a masarautar nan. Saida suka fito daga masarautar a d'arare sarkin mota yace, “ranka ya dad'e ina muka dosa?”. Tamkar bazai tankaba, sai kuma can afusace yace, “plaza!”. “angama Ranka ya dad'e, ALLAH ya huci zuciyarka ya shugabana”. Banza yamasa bai tanka masaba, sai huci yakeyi yanna karkad'a k'afafu da taunar lips, idonsa yayi zajur saboda masifar 6acin rai. A plaza ma tunda yashigo kowa ya fahimci yanda cikin 6acin rai, Dan ko kallon masu gaisheshi bayayi, mutane masu siyayya sai kallonshi sukeyi, dama wasu gulmace takawosu dansu k'ara ganema idonsu akan labarin da ayau yazaga ko'ina da ina. kai tsaye wani Office yashiga. Cikin hanzari Wanda yake a office d'in yamik'e domin kwasar gaisuwa, sai dai yanayin ogan NASA yayi masifar rikitashi. Bai saurari gaisuwarba yace, “inason ganin abinda yafayu a CCTV tundaga safiyay jiya hay daye”. Jiki Na rawa guy d'in yace “angama ranka ya dad'e”. Kujera ya jawoma Galadima ya zauna, sannan yagyra zaman computers d'in wajen sosai, tariyo wa yafarayi cikin nutsuwa, saida yadawo Sunday morning 6pm sannan ya saki, tundaga bud'e plaza har zuwa masu share-share da goge-goge dasukayi aikinsu, har lokacin da masu sayayya suka fara Shiga da fita a plaza d'in, har an wuce yace “dawo baya kad'an”. A slowly yadawo bayan kad'an, har zuwa kan wasu samari biyu d'aya sanye da jallabiya d'ayan wandon Jeans da farar t-shirt. “kayo zooming d'in yayannan dake tsaye sunan waige-waige”. Zooming d'insu yayi, sannan yasanya play yanna tafiya a slow. Samarin sunata 'yan kalle-kallene, saikuma zuwa can d'aya yasaka waya a kunne yana magana da kallon cctv camera d'in dake hasko tsakkiyar plaza d'in Inda motoci ke Parking, saikuma ya janye idonsa ya maida kan motocin dakeJere a wajen. da ganin Kasan yana maganane, Dan d'ayan dasuke tare yanata gyad'a Kansa alamar gamsuwa da abinda d'an uwansa yake fad'a. Galadima Na zaune shiru, idonsa nakan computers d'in yana nazarin gayun har aka wuce Kansu, baice uffanba yacigaba da kallon shigi da ficin jama har zuwa 8:11pm, daga nan Computer tayi d'iff. Da Sauri Galadima ya kalli sarayin “mi yake fayuwane?”. “Ranka ya dad'e wlhy nima ban saniba, amma bara Na duba”. Danne danne saurayin yafara da 'yan dube-dube, babu wata matsala daga nan. Kallon Galadima yayi yace “ranka ya dad'e babu wata Matsala daga nan, sai dai Idan daga cameras d'inne”. A tsawace yace “bangane mikake nufi daga cameyas d'inne ba!? Kenan hay shigowata jiya babu kenan!? kuma kana zaune a office amma bakayi complain ba tun ajiyan? mika aikata!!? mi suka baka ne domin tozarta ni!!? nace nawa suka baka Saleem!!!!?”. Kusan duk Wanda ke cikin plaza d'inan a yau yaji wannan hargagin Na Galadima. Jikin matashin saurayin ne yafara rawa, ya zube a k'asa gaban Galadima saboda tsabar tsoratar dayayi da yanayinsa, tunda yake aiki a k'ark'ashinsa baita6a ganinsa cikin wannan yanayin irin Na yau d'inna ba, duk da labarin abinda yafaru yazo kunanensu, sunkuma ganin a jarida da social media baiyi zaton lamarin zaiyi zafi hakaba. “wlhy yalla6ai babu Wanda yakeda abinda zai sayeni na cutar dakai, Kaine ka ceci rayuwata daga garari, ka tallafi maraicina a lokacin da nake Neman lalacewa saboda rashin matallafi, kazama gatana nida mahaifiyata da k'annena, mizaisa nabiyema rud'in wasu akan 6ata maka suna....” “ya Isa haka!!”. ‘galadima yafad'a cikin tsawa’. Gaba d'aya Galadima ya birkice musu a plaza, yasa securitys d'in wajen da dogaransa sun kori dukkan masu sayya dake ciki, ya tartare ma'aikatan wajen a d'aya, ya tabbatar musu da in har munafukan cikinsu da aka had'a baki dasu basu fidda kansuba gaba d'aya sai sunyi dana sanin saninsa. Kaf d'insu sun rud'e, sai rantse-rantse da k'ok'arin kare Kansu sukeyi, amma yak'i saurarensu, ganin zasu kuma dagula masa lissafi saiya basu suspension kawai aka rufe plaza d'in baki d'aya. Motocinsa Na k'ok'arin barin wajen motar Muftahu tashigo. Muftahu ya faka motarsa waje d'aya suka fito shida Harun, (shima Harun abokin Galadima ne makusanci, Dan zan iya cewama yafi sanin sirrin Galadima fiye da kowa a abokansa gaba d'aya, shi d'an waziri ne). Tunkan su k'araso Galadima ya sauke glass d'in motar da kansa. kallo d'aya sukai masa duk suka tsorata, Dan basu ta6a ganinsa a irin wannan 6acin ranba, baice uffanba, sai nuni daya musu akan su shigo motar. Basu musaba suka bud'e suka shiga, Muftahu a gaba, Harun yashiga baya kusada Galadima. Bayan gaisuwa dasukayi garesa babu Wanda Yakuma cewa komai, Dan ko gaisuwar bai amsa musuba, hannu kawai ya d'aga musu. Sun hau titi sarkin mota yace “Ranka ya dad'e ina muka dosa?”. ‘cikin girmamawa da taka tsantsan yay maganar”. Murya a shak'e yace “gidan Jayiday”. Sarkin mota bai fahimtaba, amma yana tsoron tanbaya, murya k'asa-k'asa ya tambayi Muftahu ”. Murmushi kawai Muftahu yayi yana girgiza kai, shiya shiga yima sarkin mota kwatance har suka Isa..... ★.★.★.★.★.★.★.★.★.★ Muna tsaka da barci saboda allurar da doctor yamana Innaro tafad'o d'akin, babu ko tausayi tashiga tashinmu cikin d'ad'd'aka mana duka a baya da cinyoyinmu. Dagani har Munubiya a firgice muka tashi zaune. “kutashi munafukai, Ashe abin ba a iya runguma da kama hannu ya tsayaba harda ciki kuka kwaso mana?, tsinannun gayyar tsiya, wlhy dagaku har uwarku yau saikin bar gidanan, a yau d'inan idan ubanku bai saki uwarkuba kun tattara kun tafi saina tsine masa albarka, yazo yaza6a ko Ku ko ni yau agidanan. sai kuma tafashe dakuka, takama bakin zaninta datayo lullu6i tana sharar hawaye, “kai ni dai Malam ya cutar dani akan had'a wannan aure da d'iyar marasa asali, ai gashinan ta Haifa mana bala'i da masifa, shikuma yatafi yabarni da kunyata, Malam kacuceni katafi kabar mana baya da k'ura. Wlhy yau sai A'isha tabar gidanan itada gayyar tsiyar 'ya'yanta, natsaneku daduk wandama zai soki A'isha, natsaneku wlhy, takuma fashewa da kuka. Tuni matan gidanmu kowa yafito, wasu harsun shigo falonmu, wasu kuma Na daga k'ofar d'aki, harda tsirarin 'yan biki da sukak'i tafiya domin tsayawa kallon kwaf. Cikin matan gidanmu ne wata taje tasanarma innaro wai bamuda lafiya munata amai duk abinda mukaci, anakiran likita ya dubamu yace duk munada ciki wata uku-uku. Ni da Munubiya mun had'e kai muna kuka mai tsuma rai saboda tozarcin da innaro kemana muda mahaifiyarmu agaban bainar jama'a. Dady da Abba k'aramine suka shigo sunama innaro magana akan bafa haka zancen yakeba, babu Wanda yace munada ciki. Hayayyak'o musu tayi tana zaginsu, wai k'aryane suna kare Innarmu ne, aida likitan bai fad'aba baza'aje a sanar mata ba. Cikin 6acin rai baba k'arami yace, “inna waye yaje yafad'a miki wannan maganar to?”. “cikin matan gidanan mana, kuma daga bakin wadda nasan bazataimin k'aryaba”. Ran Dady ma a wannan karon ya 6aci, afusace yace, “inna wacece acikinsu? Wace 'Yar isakar matace”. Nanafa matan gidanan mu suka shiga raba idanu akan juna. Innaro tace “karka kuma zaginta, idaba ayiba bazatace anyinba, kuma koma wacece bazan fad'aba, idan kuma ni kake zagi sainaji?”. “ALLAH ya huci zuciyarki inna, ni yaza'ayi Na zageki”. “kai dai kasani sakarai”. Duk abinda ke faruwa Abbanmu da Innarmu Na saurare daga d'akinsa amma acikinsu babu Wanda yayi yunk'urin fitowa. Kayanmu innaro tafara kwasa tana watsowa waje, wai saimun bar gidan. “Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un, wannan wane irin tashin hankaline?”. ‘innarmu tafad'a cikin matsanancin kuka’. Rungumeta Abbanmu yayi shima yana k'ok'arin maida kwallar data cika masa idanu. Ganin abin yana Neman wuce gona da iri baba k'arami yafita da hanzari, wani tsoho dake can k'asan layinmu yaje ya d'akko, tsohon abokin Malam faruku ne na k'ut da k'ut, shika d'aine zai iya takama Innaro burki kuma. Aiko hakance ta kasance, tunda yashigo yay magana Innaro ta dakata da abinda takeyi tana huci da fidda numfashi. Tsoho Malam Labaran yace, “haba innar jafaru, da hankalinki da girmanki kike aikata wannan abin Na yara a gaban sirikanki da 'ya'yanki da jikokinki? Shin babu mai fad'a miki kijine wai kekam?”. Cikin sassauta murya tace, “malam mai kanwa nasan bakasan ainahin abinda yafaru bane kaima, amma wlhy da dakanka zakace Auwalu yasaki marar asalinnan sukama gabansu itada 'ya'yanta am.....” Hannu ya d'aga mata, yagyara tsayuwarsa jikin sandarsa dake taimaka masa tafiya, naji komai innar jafaru, amma wannan hanyar da kuka biyo ba wai itace mai 6illewa ba, bincike yakamata ayi domin asan gaskiyar lamarin. dan haka zoki wuce gida, zuwa gobe zamu tattauna akan lamarin sannan kowa ya nutsu, mukuma jira abinda zai fito daga can gidan Sarkin”. Badan innaro tasoba tafice, hakama matan gidanan mu basuso wasan yak'are iya nanba, sunso a yau Innarmu tabar gidan da saki, sannan mukuma mahaifinmu ya koremu. Kowa taja k'afa takoma d'akinta cikeda takaici da addu'ar ALLAH yasa daga gidan sarkin suma su d'auki mummunan mataki akanmu..... Maman fauziyya Ce kawai ta nuna damuwarta akan lamarin ★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★ Su Galadima ma sun isa gidan jaridar *Manuniya* tun sanarwar isowarsa ta kad'a hantar cikin ma'aikatan wajen, musamman wad'anda basuda laifi akan lamarin, tirsasu akayi. Shi kansa manaja d'in wajen a kid'ime yake, dukya rikice yarasa matsugunni har Galadima da gayyarsa suka iso office d'in bisa jagorancin sakatare d'insa. K'asa yazube kawai yana kwasar gaisuwa wajen Galadima, ko kallo bai ishi Galadima ba, cikin daka tsawa yafara magana...........✍🏼 Tofa masu karatu, ko manajan jaridar MANUNIYA zai amsa laifinsa? Kokuwa zai fad'i wad'anda suka sanyashine inba laifinsa bane shima? to koma dai shima da had'in bakinsa?. Wane mataki masarautar su Galadima kuke ganin zata d'auka akansa? Shin ina ma maganganun Momma suka dosa ne? Miya faru da mahaifin Galadima har suka koma k'asar India da zama?.😕 Kumuje zuwa my guys danjin yanda zata kaya. da amsoshin d'unbin tambayoyinkun nan.⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀🤾🏻‍♀ _Naga mutane basa fahimtar yaren yarima😂, yarima later R ne baidashi, bawai tsamin bakine dashiba fa, kun gane, naga wasu kamar suna zaton tsamin bakine dashi🤣._ _Ngd da comments d'inku, kuna sakani farin ciki sosai, kuyi hak'uri da rashin amsawa ta, kunada d'unbin yawane wallahi😊🥰🥰🥰🥰. I love you wujiga-wijiga all😁✋🏻._ *_Ya ALLAH ka gafarta ma iyayenmu_*😭👏🏻 [4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* __________________________ *_Naga idi🙆🏻, Galadima fa ba tsamin baki bane dashi, Ku fahimta😂, bashida (R) ne, amma gashinan nayi gyara, ina fatan yanzu zakuna fahimtarsa🤣._* _______________________________ 👉🏻1⃣1⃣ .........Ba manager kawaiba, hatta da sauran jama'ar dake gidan jaridar saida suka tsorata da tsawar Galadima, su Muftahu ma tsorone ya kamasu, sunsan irin wannan matsanancin fushin gareshi babbar matsala ce ga lafiyarsa. Aikam sai gashi ya dafe kansa, saboda yay wani mugun sara masa, da sauri Harun yajawo kujera ya kamashi ya zaunar, har yanzu dafe yake da kan nasa. Muftahu ya furzar da hucin, matsalar da suke gudun ta d'akko hanyar faruwa kenan. kallon manaja dake durk'ushe har yanzun yayi, yace “tashi ka zauna”. Mik'ewa manaja yayi jiki Na rawa yakoma saman kujera, Muftahu da Harun ma suka zazzauna. Cikin tsare gida Harun yace, “manager ka nutsu, kabamu had'inkai wajan fad'ar gaskiya, inba hakaba wlhy zakayi nadama ne, ba kaiba hatta da ahalinka saisunyi nadamar kasancewarka acikinsu”. Manaja yashare guntun kwallar dasuka taru masa a idanu, a nutse yafara fad'in “ai tunkan jaridar jiya tafita nake acikin nadama, nayi dana Sanin kasancewata ma'aikacin jaridar da aka ci zarafin d'an Wanda yay tushen kasan cewata a wannan matsayin danake, da ace remote d'in rayuwata a hannuna yake, dana tariyo bayana jiya bata shigo rayuwata ba, amma Na.....” Muftahu ya katseshi cikin d'aga masa hannu “kaga manager, ba rayuwarka mukazo saniba, munason ka fad'a mana waye yasaka wannan aikin? nawa suka biyaka kamusu shi?”. “wlhy tallahi yalla6ai basu biyani komaiba, kaga wacan jakar sune suka ajiye min ita, amma ko bud'eta banyiba. kuma babu wani ma'aikaci daya buga labarinan agidan jaridar nan da hannunsa. sune da Kansu adaren jiya sukayi komai, bayan sun had'emu waje guda da bindugu, kuma sunzo nannane dukansu fuska arufe, wlhy ko fuskar mutum d'aya bamu ganiba, yanzu haka sun kwashe muhimman documents dake ma'aikatar nan sun tafi dasu. kuma sunsan da zuwan yalla6ai gurinnan yau, Dan komai sunyishine a tsare kamar yanda mukaji suna hira a tsakaninsu” manaja ya fashe da kuka, sannan yacigaba da fad'in “saboda sunsan zakuzo nan yau, sunje gidana tun adaren jiya, sun kwashemin iyali da mahaifiyata, yanzu haka suna wajensu, sun tabbatar min inhar wani magana yafito abakina abakin ran matata da yarana hud'u da mahaifiyata sai k'anwata. wlhy ina cikin masifa, yau anan Na kwana, nakasa fita waje saboda banason jin 6atancin da jama'a suka gani a wannan safiyar akan yalla6ai. Wlhy Na rantse muku bansan komaiba”. Tunda manaja yafara magana kowa yay tsit, Galadima bai d'agoba saida yaji manaja ya ambaci iyalansa Na wajen wad'anda suka aikata aika-aikar. Idonsa yakad'a yayi jazur, sosai manaja ya tsorata da idanun Galadima, haryana tunani a zuciyarsa anya Galadima shi kad'aine, bashida aljanu kuwa?. Komai Galadima bai ceba, ya tashi dafe dakai yafice daga office d'in, ma'aikatan wajen sai zubewa suke suna kwasar gaisuwa, amma kallon kowa baiyiba yafice. Dogaransa suna ganinsa suka mik'e da Sauri, Mota suka bud'e masa yashiga, suma su Muftahu suka fito da hanzari. ★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★.★ Tun daga fitar innaro sai gidan yay tsit, kowa ya kama gabansa zuwa d'akinsa, a can suka cigaba da gulmace-gulmacensu suda bak'insu. Niko da Munubiya muka shiga raira sabon kuka, munubiya ta kamo hannuna ta rik'e anata. “Munaya dan girman ALLAH kibarni Na kar6i hukuncin laifina, nice Na aikata bakeba, miyasa zaki cema iyayenmu kece? kibari nafad'a musu gaskiya please ”. “A'a Munubiya, wannan laifin nawane, karki manta ta sanadina abinnan yafaru, da ace Fu'aad bai kaimu plaza d'innanba da hakan bata faruba wlhy, munubiya farincikina fansane agareki, har abada bazan iya juriyar ganinki cikin k'unciba, Dan Girman ALLAH koda da wasa kar wani agidannan yaji banice Na aikata abunnanba koda kuwa innarmu Ce, namiki alk'awarin zan jure duk wata fitina dazata taso, zankira Fu'aad yafito muyi aure, duk da naso ace rana d'aya aurenmu zai kasance, amma haka ALLAH ya k'addara mana”. rungume juna mukayi muka kuma fashewa da kuka, cikin shashshekar kuka Munubiya ke fad'in “mi mukaima Wanda ya k'ulla mana wannan sharrin? mi muka tare masa agidan duniyarnan Munaya?”. “ban saniba Munubiya, bansan waneneba? Amma nafi zargin gidan wannan jaridar, aganinsu sun sami babban labari, bara su buga suyi suna, Sun zaluncemu Munubiya, sun yad'a labarin abinda ba haka faruwarsa ta kasanceba, Galadima ko ta6aki baiyiba amma suka saka har yana kissing d'inki, wane irin zaluncine wannan? wlhy nima bai ta6a niba da mukayi karo a filin idi, amma ki duba hannunsa rik'e da nawa ajaridar, Munubiya banga laifin iyayenmu ba, kowanne mahaifa bazasu so ganin wannan mummunan abinba, kuma ko zamu kwana rantsuwa bakowa zai amince damu ba, INA tausayama innarmu, ada Yaya muka k'are ma a gidannan bare yanzu?, munubiya innarmu innarmu, banason innarmu tashiga mummunan hali akanmu, yazamuyi innarmu ta fahimcemu, koda ace kowa bai yarda damu ba inason innarmu fahimcemu munubiya.....” “Na fahimceku 'ya'yana, tabbas nashiga tashin hankali da ganin hotonku a jarida, kuma a yanayin da kowace uwa ba zataso ganin 'ya'yanta a wanna halinba, kuma ace bazata shiga fiyeda yanayin Dana fad'aba, sai dai ni ba abinda naganine yasakani cikin rud'ani irin haka ba harna yanke jiki na fad'i, cin zarafin innaro ne. 'ya'yana nasan bazaku aikata koda makamancin hakanba, dan naji ajikina sharri akai muku.....” Da gudu suka sakko a gadon sukazo suka fad'a jikin innarsu suka cigaba da raira kuka harda ita kanta innar, saida sukayi mai isarsu sannan sukayi shiru. Duk suka nutsu suka mata bayanin komai, har Munaya ta d'akko wayar da Galadima ya barta da ita a filin idi ta nuna musu. Nanna INA ta kuma fahimtar akwai 6oyayyen al'amarin abinda basu saniba akan lamarin, kuma tafi zargin k'ullin Anma Galadima ne kawai, 'ya'yanta k'addara Ce ta sakasu cikin sark'ak'iyar, itadai Addu'arta ALLAH ya fiddashi da 'ya'yanta baki d'aya, saitaji yabata matuk'ar tausayima. Suna cikin haka saiga mama Rabi'a dasu Ayusher, nanma aka kuma zaman warware zance, mama Rabi'a da inna suka kuma fahimtar komai yanda yake. Nasiha suka Shiga yima 'ya'yan Nasu mai ratsa jiki, sannan suka nuna musu illar biyema samari batareda wani dogon tunaniba, duk sai jikin su Munaya yayi sanyi, sun fahimci bin Fu'aad dasukayi plaza shine yazama babban kuskurensu. Sun nemi gafarar iyayen nasu akan hakan dasuka aikata, daganan suka Shiga tattauna maganar Auren munaya da Abba yakafe akan nanda sati biyu. Sun Yanke shawara akan akira Fu'aad, inhar da gaske yakeyi to saiya fito kawai. Akan wannan shawarrar suka zauna gaba d'aya. ★★.★★.★★.★★.★★ Har suka Isa cikin masarautar Galadima baiko motsaba, yana tangad'i da layi yashige 6angarensa, daga Muftahu har Harun babu Wanda yayi yunk'urin binsa. Tunda yaje yazube saman 3seater bai sake sanin inda kansa yakeba saboda matsanancin ciwon kai dake damunsa, da k'yar ya iya gabatar da sallar magrib da isha'i a lokaci d'aya, a saman abin sallar ya kwanta rigingine dafe da goshi, yana kwance shiba mai barciba shiba ido biyuba. 8:30pm dukkan mai ruwa da tsaki a meeting d'in ya hallara, hatta da sarki gaba d'aya, sai dai kuma babu Galadima babu dalilinsa har mama Fulani tafito. (Babbar magana 😨) na fad'a a raina, saboda ganin tsantsar mulki da isa ajikin hamshak'iyar tsohuwa dazata iya kaiwa shekaru 77 a duniya, sai dai tsantsar hutu da gayu ya 6oye ziryan d'in tsufan nata, gata da k'aramin jiki kuma, daka ganta haka bafulatanar asali. Tunda ta fito kowa a falon yamik'e tsaye saboda girmamawa a gareta, amma banda sarki, ya risinar da kansane kawai alamun girmamawa ga mahaifiyar tasa. Saman kujera 2seater ta zauna cikeda izzar mulki, (saikace itace sarkin🤦🏻‍♀) sai da ta gamaima kowa dake falon kallon tsaf sannan takuma kamewa, cikeda k'asaita tace, “Shi yana ina? Ko raini. Hankalin nasane ya hanashi zuwa?”. Kowa dake wajen yasan galadima take nufi, babu wanda ya iya cewa komai sai wani matashin saurayi dazasu iya zama sa'annin juna da galadima, ya gyara zamansa yana wani 6ata rai shima, “Granny kinsan halinsa aii, ba ganin kowa da gashi yakeba a masarautar nan mtsoww”. Mama Fulani ta turo hanci ga bada, cikeda fushi ta bada umarnin a kira mata jakadiya. babu dad'ewa saiga jakadiya tashigo, k'asa ta zube tamkar zatayi mata sujuda tafara fad'in “ALLAH yaja zamaninki ranki ya dad'e, kinga taki kinga tawasu, fatanmu kiga tawasun wasuma, Sarautar gagara badau a hannunki take, domin kaida kaya ai duk mallakar wuyane, duk mai shirin ganin barcinki ya tabbata shima bazaiyi nasaba, kece k'i gudu samaza gudu, jaruma mai dad'and'en tarihi, kin ajiye tarihin da babu wanda yake dashi a masarautar nan, koda kuwa mai martaba gagara badaune, ALLAH ya tsare gabanki ya tsare bayanki, mace mai kamar maza, mazanma a tafin k'afafunki suke ya uwar gijiyata”. Sosai kirarin jakadiya yayima mama Fulani dad'i, takuma kishingid'a a kujerar, cikeda izza tace, “inason ganin Galadima yanzunan”. Angama damusa k'i sabo, cika umarninki wajabtaccene a gareni 'Yar sarki, matar sairi kuma mamar sarki, wata ran kakar sarki, ki huta lafiya babbar giwa”. Fita jakadiya tayi. Ta isa 6angaren galadima, inda sarkin k'ofa yashiga domin yimata iso, halin daya isake shugaban nasa ya razanashi, amma haka yadake ya isar da sak'on jakadiya. Da k'yar galadima yay masa nuni akan yabarta tashigo. Babu dad'ewa saiga jakadiya, ta rusina cikin girmamawa ta gaisheshi, bata damu da rashin amsawar tashiba ta isar da sak'on mama Fulani. hannu kawai ya iya d'aga mata. Kusan mintuna 7 da fitar jakadiya yamik'e dafe da kansa dayakejin tamkar zai fad'o k'asa, jiyay falon na juya masa, ya dafe bango da gyar kusan 2munute sannan yad'an lafa, haka yafito yana d'an tangad'i, wajen mota yanufa, dan bazai iya zuwa sashen mama Fulani da k'afaba, saboda akwai tazara sosai a tsakaninsu. Da sauri sarkin mota yataso ya bud'e masa, shima shiga yayi mazaunin driver, sauran dogaranma suka shishshiga mota. Da k'yar galadima yafurta “sashen mama Fulani zamuje, sauran su zauna”. cikin girmamawa sarkin mota ya amsa, sannan ya sanarma sauran dogaran. dukkan jama'ar dake falon idanu suka zuboma Galadima daya shigo dafe da kansa, baima kowa magana ba yasamu can gefe ya zauna, har yanzu hanunsa na saman kansa, muryarsa a shak'e yace, “barkanku da dare”. Hakan yayi masifar k'ona ran mama Fulani, saboda ma ya rainata tare zai gaidata da kowa? kuma bazaizo gaban taba ma yabata girmanta?. A falonma wasu sun amsa wasu basu amsa mishiba, shi baima San sunayiba, ta kansa kawai yakeyi. Cikeda izza mama Fulani tace, “to isashe, gaisuwar ma saina rok'a ko yaya”. Dukda halin dayake ciki bai hanashi sakin guntun murmushiba, ya janye hannunsa daga goshinsa, idanunsa dasuke matuk'ar jajur yad'ago ya kalleta, ba mama Fulani niba kowama a falon ya firgita daganin idanunsa, hakan ya tabbatar musu da bashida lfy kenan. Ahankali Yakuma furta “bagykanki da hutawa”. “ALLAH yarabamu da bak'in hali” . ‘mama Fulani tafad'a batareda ta amsa gaisuwar ba’. Baice uffanba ya maida kansa ya duk'ar, tareda kuma tallafe goshin yana ta6e baki. Idanun Ummu Hasheem yacika da kwalla saboda tausayin Galadima, ko kad'an batasan bashida lafiya ba, dukda d'azun ta aika bayinta su duba matashi suka tarar yafita. Mama Fulani kam baki ta k'ya6e tareda kuma hard'ewa a kujera, takai dubanta ga wani dake gefenta, Matawalle! ahad'amin video call da Zeenah yanzunan”. “angama ranki ya dad'e” Dan danan yahad'a video call bayan yakira wata number, wata kamilalliyar matace ta bayyana ajikin System d'in, tana sanye cikin shigar kamala, kallo d'aya namata Na hango kamannin Galadima tartare da ita, dukda kamar tafisa haske, hakkane ya tabbatar min da Momma ce. Cikin girmamawa ta gaida mama Fulani, ita kuma ta amsa cikeda k'asaita sannan tafara magana kamar haka. “nasan kowa yasan miya taramu anan wajen?, bana buk'atar maimaita wannan shed'ancin a harshena, wanda kuma ya aikata yasan kansa, Dan haka hukunci biyune, yanada za6i aciki. Na farko tozarcin da yayama masarautarnan da zubar mana mutunci mun haramta masa auren kowacce yarinya data fito daga kowacce masarauta, na biyu ya gaggauta fidda matar aure acikin shekararnan kafin yaje yayma wata ciki a waje akawo mana d'an tsakar gida a masarauta, kokuma mu muza6a masa acikin bayin gidannan, hukunci na farko babu sasauci acikinsa kuma babu canji, Na biyu yanada za6i nemowa komu nema masa. Wannan shine tabbataccen hukuncin kotun fulani. Idan akwai mai abun fad'a sainaji?”. Kowa ya girgiza kai alamun a'a, wasu hukuncin bai musu dad'iba, wasuko yamusu fiye da zaton mai karatu. A hankali Galadima ya yunk'ura yatashi batareda yacema kowa uffanba yanufi hanyar fita. “to fand'ararre, daka tafi ba'a gama magana ba ai uwarka zataji, mara mutunci mai bak'in hali”. Juyowa Galadima yayi ya kalli mama Fulani, wani k'asaitaccen murmushi ya sakar mata sannan yay salute nata yafice abinsa”. Mafi yawansu saida suka zaro idanun mamakinsa, dama Kowa yasan galadima baya tsoron mama Fulani a masarautar, duk masifarta saima yagadama yake amsata, gaisheta kam saiya zo k'asar yatafi ma bata ganshiba. Iya kacinta tayi masifarta da sababi ta hak'ura, babu yanda ta iya dashi. Murmushi kawai shima sarki yayi baice komaiba. Mama Fulani kam kasa koda motsi tayi a kujerar saboda abin kunyar da galadima yayi mata gaban kowa, ta tsani shed'anin yaronnan mai ido a tsaitsaye dabaya shakkar kowa. Kwafa tayi sannan tatashi tabar falon tana tafiya cikeda mulki da izza. Gaba d'aya suke fad'in ALLAH ya huci zuciyar sarauniyar sarakuna. Duk abinda ke faruwa Momma naji kuma tana gani, amma dayake Galadima yana bayan laptop d'in bataga miyayiba, hasalima bataji ko sau d'aya yayi magana ba, hakanne ya tada hankalinta, mama Fulani Na barin wajen ta katse call d'in, waya ta d'auka takira number Galadima, amma harta tainke bai d'agaba. Kira Na biyu ta sakeyi, hakan yay dai-dai da shigowar Galadima falon dafe da kansa. Da k'yar ya iya d'aga wayar, muryarsa a shak'e yace, “Momma zan kigyaki anjima” bai jira cewarta ba ya yanke wayar. Hankalin Momma yakuma tashi, tasan ransa yakai k'ololuwar 6aci, da sauri ta danna kiran Harun, yana d'agawa ko gaisuwar dayake mata bata amsaba tace, “Harun maza jeka duba min Moh'd yanzunan”. Yanda yaji Momma Na magana shima kansa saiya kid'ime..... ★.★.★.★.★.★.★.★.★.★ Ayusher tafita tasiyo min credit domin kiran Fu'aad. Jikina a sanyaye nagama loda katin, tunani nakeyi shin Fu'aad zai kar6eni bayan yaji abinda yafaru a jiya zuwa yau? tunda komai akan idonsa yafaru. Na dad'e ina juya wayar a hannu kafin Nayi dialing d'in Number d'insa d'in, harta tsinke bai d'agaba, ban damuba Na sake kiransa da tunanin ko baya kusa da wayarne. Bugun farko kuwa ya d'aga wayar...........✍🏼 Humm masu karatu, mi kuke tunanin zai faru tsakanin Munaya da Fu'aad a waya, zai kar6eta kokuwa sa6anin haka?. Yaya zata kasance ga Galadima kuma?. Wannan amsar tana a page 12 da zaizo muku ranar Monday😃👌🏻. Barkanku da juma'a. Musha weekend lafiya🤝🏻🥰🥰. Team *_INNARO & MAMA FULANI_*🥴🥴⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu._*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉1⃣2⃣ .......Murya a sanyaye Munaya tace, “Assalamu alaika”. “wa'alaikissalam”. ‘wata murya ta amsa sa6anin Fu'aad’. “Uhhm 'yar uwa please, ko ina mai wayar dan ALLAH?”. “Mai wayar kuma? ai nice mai wayar”. Wani iri munaya taji a zuciyarta, suka kalli juna itada Munubiya dan a Hans free tasaka wayar. alama munubiya tamata akan tayi magana. kai Munaya ta jinjina mata, sannan tace, “ayya 'yar uwa sorry dan ALLAH, wlhy wanine yabani number d'innan mai suna Fu'aad”. “Fu'aad!”. ‘yarinyar ta maimaita daga can’, saikuma tace “to gaskiya 'yar uwa yabaki wrong Number, ni sunana Afnan, ina Katsina state ne”. Wasu hawaye masu zafi suka zubo a kumatun Munaya, “shikenan ngd sis..., kiyi hak'uri”. “no babu damuwa”. Bayan Munaya ta katse wayar ta dafe kai tana hawaye, daga Ayusher har Munubiya basa Neman k'arin bayani, tunda sunji komai, Munubiya ta share hawayenta tana murmushin takaici, “kibarshi karki sake kiranshi, nasan shine yabama yarinyar nan wayar akan tace wrong number ne, ya ALLAH ka kawo mana sauk'i a wannan lamari dai”. Tsaki Ayusher taja, ta kamo hannun Munaya “sweet sis..., please wannan karya zama abinda zai ta6a zuciyarki, ki d'auki hakan matsayin ba komaiba, kuma hakan da Fu'aad yayi yasani kuma tabbatar da zargin danake a kansa, ku duba yanda yazage saimunje birnin gayu plaza aranar”. Gaba d'ayansu zuba mata ido sukayi cikin wani yanayi. Feena dake kwance tatashi zaune, “humm aini wlhy tunda zancen jaridar nan yafito zargina yana kan Fu'aad ne, Na barine akirashi dama danna sake tabbatarwa”. Munubiya tace, “sisters nifa duk Na kasan fahimtar zancennan naku fa, zargi babu k'yau ai, miye ribarsa idan ya aikata hakan? dukama yaushe muka San juna dazai yi hakan a garemu? yarasa kuma dawa zai mana hakan sai galadima?”. Zama Ayusher ta gyara, tafara musu bayani dalla-dalla. “tad'ora da fad'in kinsani ko saboda galadiman yayi?”. “to amma Dan zaima Galadima mu miye Na had'awa damu kuma?”. “wannan amasar tana wajen Fu'aad sister ”. Hankalin Munaya yatashi ainun, itafa ko kad'an bata ta6a kawo Fu'aad acikin wad'anda take zargiba, amma maganar Ayusher tasata dogon nazari yanzu, duk da dai bawai tama yarda baneba kwata-kwata.. ★★★★★★★★★★ Lokacin da harun ya iso sashen Galadima bai wani jira isoba yashiga, kwance ya iskeshi bisa 3seaters sam6al, hannunsa d'aya dafe da k'irji, d'aya dafe da kansa. Da sassarfa ya k'arasa gabansa “Sameer lafiya kuwa?”. Da hannu Galadima yamasa nuni da k'irjinsa da Kansa. “ya salam, Sameer! Shiyyasa naketa cemaka kacire abunnan a ranka, kafasan matsalarka batason yawan takura da tunani”. Wayarsa dake ringing ya Ciro a aljihu, Momma Ce ke kiransa. Cikeda girmamawa ya amsa sallamar data masa, sannan naji yace, “wlhy Momma bashida lfy, kuma k'irjinsa yake complain akai”. “ok Momma ”. Yana yanke wayar sai yayi kiran Dr Jalal. “Jaalal please kana gida kuwa?”. Bansan wace amsa ya bashi ba daga can, naji dai yace, “please kazo kaduba Galadima”. Babu dad'ewa saiga Dr Jaalal, damuwa sosai Nagano a fuskarshi saboda ganin halin da Galadima yake ciki. Harun ya taimaka masa suka kaishi bedroom, sannan yamasa allurar barci. Babu dad'ewa kuwa barcin ya kwasheshi. Su duka ajiyar zuciya suka sauke, Dr jaalal yama harun sallama yatafi. Yana fita Muftahu Na shigowa, gaisawa sukayi da Harun, sannan ya tambayi jikin Galadima d'in. Harun ya amsa masa Cesar da sauk'i. Anan sashen Galadima suka kwana, sai dai kowanne acikinsu da dalilin kwannan nasa. *_Washe gari_* Alhmdllh Galadima yatashi jikinsa da d'an sauk'i, yakuma ji dad'in ganin Harun da Muftahu a tare dashi. bai iya zuwa masallaciba sai a d'aki yayi salla. Yana zaune akan sallayar yana azkar su Muftahu suka shigo, zama sukayi bisa Sofa suna jiran yak'arasa azkar d'in nasa. Bayan ya k'arasa ya juyo garesu, hannu ya mik'a musu sukayi musabaha, suka tamyashi jikinsa. Yace da sauk'i Alhmddlh, sannan yace, “Muftahu inason ticket, dan yau zan wuce India, ina buk'atar ganin doctor d'ina”. “ok babu damuwa, bara na bincika idan akwai jirgi mai zuwa India daret”. Harun yamik'e yana fad'in “bara ahad'a maka ruwan wanka to”. Kai ya d'agama harun, ya maida idonsa ya lumshe tareda jingina da Waldrop. Muftahu dake latsa waya yad'ago ya kallesa, “babu jirgin dazai tashi a yau, sai gobe 1:30pm”. Batareda ya bud'e idonsa ba yace, “bincika min ta Abuja ko legos. dan bazan iya kuma kwana a k'asar nanba yau, ina buk'atar ganin lilita”. Kai Muftahu ya jinjina ya cigaba da latse-latsensa a wayar, kusan mintuna 4 sannan yad'ago, “an samu, amma zai biya Abu-Dhabi ya sauke Passenger's, daga nan zasuyi hutun kamar na 1hour”. Idomsa a lumshen yace “yaushe zai tashi daga Nan?”. “12pm, yanzu na saya maka ticket d'in zuwa Abuja, jirgin zai tashi 8am ne”. “Ok bara na shirya to”. Harun dake tsaye yana saurarensu yace “bara naje Na watsa ruwa nima”. Shima Muftahu mik'ewa yayi suka fita tare. Galadima yashiga bathroom, kusan mintunansa 40 sannan ya fito, dauriya kawai yakeyi, amma shi kad'ai yasan irin suyar da zuciyarsa ke masa. tsaf ya shirya cikin Suit blue, rigarshi ta ciki Orange, yayi k'yau sosai, yana zaune bakin gado yana saka takalminsa Muftahu yashigo da sallama. d'ago idanunsa yayi akan Muftahu, sannan yatashi tsaye yana gyara belt nashi, “ya maganar binciko yarinyar nan?”. “Nagama komai, inason kasami nutsuwane sai muyi maganar daman”. Galadima dake gyara 'yar sumarsa da bawani yatarata da uban yawa bane yace “ok, katura min komai zan duba, sannan inason kaje kuyi magana da commisshiner of police akan iyalan Manager d'innan”. “ok yalla6ai angama insha ALLAH”. Sallamar Harun suka amsa gaba d'aya, ya zauna kan sofa sannan yace “amma yakamata ma'aikatan plaza su koma aikinsu, naga jama'a kamar suna fassara abin dawani Abu daban kuma”. Murmushin gefen baki galadima yayi, ya ajiye Cumb d'in hannunsa yajiyo yana kallonsa “aini yanzun kuma babu kuma ta sigar dabaza'a fassara ni ba, inaga akan mace kawai yarage jaridu su buga duniya ta ganni, so sukoma aikin su kawai”. Daga Harun har Muftahu kallonsa suke cike da tausayawa. Muftahu yace wannan d'inma kansu sukai mawa, kuma ALLAH bazai barsuba”. “insha ALLAHU”. ‘cewar Harun’. Galadima baice komaiba, sai d'an kimtse kimtsen da ba'a rasabane ya k'arasa, su Harun kam suka fice suka bashi waje. Baifi mintuna 10 ba yafito suka fice, bayan yatsaya da bayinsa na mintuna biyar, bansan miya fad'a musuba, naga dai sunata faman godiya damasa addu'a. Aka bud'e masa mota yashiga, duk wanda yake k'ark'ashimsa saikaga fuskarsa ta canja alamun baya son tafiyar tasa. Kai tsaye fada suka nufa, bayan motocin sun tsaya aka bud'e masa yafito. Shi kad'ai yashiga fadan, cike take da dukkan masu ruwa da tsaki anata fadanci. Saida ya gaida sarki, sannan ya zauna mazauninsa kusada sarkin, sauran fadawan suka gaidashi cikin girmamawa, shima ya amsa cikeda mutuntawa. “ya adalin sarkinmu yau zan koma inda na fito, saboda inason ganin likitana”. Murmushi sarki yayi, sannan ya gyad'a kai bare da yayi maganaba. Da sauri Dogarawa suka d'auka da fad'in Sarki yajika Galadima, Yakuma amsa, yana maka addu'ar sauka lfy kuma. “ina godiya da wannan alfarma”. ‘galadima yafad'a cikin rissinar da kai alamun girmamawa”. Sarki yad'an gyara zamansa, ahankali ya furta “ka gaidamin da d'an uwana da gimbiya Zeenah, insha ALLAH nima nextweek ina nan zuwa”. “ina godiya ranka shi dad'e, insha ALLAH d'an uwanka zaiji”. “gyad'a kai kawai sarki yayi”. “An gaisheka galasima, ALLAH ya tsare gabanka da bayanka, ALLAH ya kaika lafiya yabama adalin tsohon sarki lafiya, Alkairin ALLAH da ni'ima sukai a garesa, gaba dai gaba dai Galadima mai jiran gado, d'an sarki jikan sarakuna k.....”. Hannu ya d'aga musu alamar ya Isa. Ya risinar da Kansa domin girmamawa ga fada sannan yamik'e suna jera masa addu'oi, yayinda shikuma yake amsawa asaman la66ansa. Bai shiga sashen kowaba yay tafiyarsa, suna isa filin jirgi ko 20 minutes basuyiba jirgin su yatashi zuwa Abuja. Muftahu da Harun da dogaransa suka dawo cikeda kewarsa. Koda ya isa Abuja hotel yanufa kai tsaye, yakama d'aki danya huta, akwai kusan 3hours nan gaba kafin jirginsu ya tashi. Rigar suit d'insa yacire tareda tie d'in, sannan ya zame wandon da rigar cikin ya kwanta dagashi sai boxer da vest. Juyi kawai yakeyi agadon, Dan barci yakasa d'aukarsa, abinda yafaru a kwanaki biyunnan yakasa barin zuciyarsa, yarasa wane irin hasashe zaiyi ga masu aikata masa hakan... Ringing d'in da phone nasa tayine yasakashi bud'e idanunsa, wayar yajawo yana kallon mai kiran. *_Sweet papi_* yagani ajikin wayar, yay saurin d'agawa kafin ta tsike. Cikeda girmamawa tamkar yana a gabansa ya rissinar da kansa bayan yatashi zaune, “Barka da hantsi ranka ya dad'e”. Daga can aka amsa “da yauwa Muhammad, ina fata kana lfy?”. “Alhmdllh ranka ya dad'e”. “To masha ALLAH, dama mamanka Ce takirani takemin wasu bayani, duk da kafin kiran nata dama naga zantukan dake yawo a jaridu da yanar gizo, zuciyata bata yarda zaka aikata hakanba Muhammad, amma inason sanin gaskiyar zancen?”. “wlhy ranka ya dad'e sunyi hakanne kawai domin 6atamin suna, amma ainahin abunda yafaru shine.............” Nan Galadima ya zayyane masa komai. Murmushi mai sauti tsohon yayi, har Galadima Na jiyosa, sannan yace, “hummm! to yanzu kai kana wace nahiya ne?”. “Ina Abuja zan koma India, saboda jikina yana Neman motsawa”. “to to, hakanma dakayi dai-daine, amma a kwantar da hankali, komai mai wucewane, komai kaga yafaru da d'an Adam rubutaccene a littafinsa, dama ita rayuwa tana tafiyane da k'addara, yanzu zan isa fada, bayan kasamu nutsuwa idan kaje zamuyi magana, duk da watak'ilma nashigo ganin mahaifin naka k'arshen watannan”. “to shikenan, ngd sosai, ALLAH yak'ara tsahon rai da lafiya mai amfani”. “amin ya rabbi Muhammad” cikin tsokana tsohon yace “kaga d'annema, duk kabi ka susuce akan k'aramin Abu, kazo Na sanmaka jarumtata mana”. Dariya Galadima yayai (karon farko danaga yayi dariya🙊😂) cikin tausasa harshe yace “haba dai, ai sai dai Na sammaka tawa, nifa sabon jinine, ta ina mai shekaru 80+ zai fi mai 29 jarumta?”. Daga canma Sarki dariya yayi, cikeda k'aunar jikan nasa, “uhmyim tunda kace haka idan kazo saimu gwada kwanji ai”. “hhh tom kafad'ama inno ta tsumaka sosai, inba hakaba zatayi takaba”. “ja'irin gora zan kamakane ai, ALLAH ya tsare hanya, ka gaida iyayen naka”. “zasuji ranka ya dad'e, a gaidamin inno, tayi hak'uri wannan karon ban shigo naci tuwon taba, nazo k'asarne da uzurori dayawa, gashima banyi ko d'ayaba”. “zataji insha ALLAHU, babu komai, adage dai da addu'a watarana sai labari, *zakaran da ALLAH ya nufa da cara, ko ana mazuru ana shaho sai yayi jikana kaji*. Murmushi Galadima yayi dan jin maganar kakan nasa, sukayi sallama cikeda k'aunar juna”. Ajiye wayar yayi yakoma ya kwanta fuskarsa d'auke da murmushi, yana k'aunar kakansa (mahaifin Momma) saboda shima yana nuna masa k'auna da kulawa, akan la66ansa ya furata “ALLAH ya k'aramaka tsawon rai my sweet papi”. Amin Galadima. ⛹🏻‍♀bara nalek'o su munaya. ★★★★*★★★*★★★★ Bansan yanda zan musalta muku irin bak'in cikin danakeba a yau, tundaga kiran Fu'aad zuwa yanzu zuciyata sai suya takemin, banida wata walwala, sai dai ina dannewa kodan kwanciyar hankalin innarmu da 'Yar uwata Munubiya, dama tun randa abunnan ya faru bamu sake fita koda tsakar gidaba dagani har 'yar uwata, abinci sai dai innarmu kosu Aryaan su kar6o mana. Habaici dai da gugar zana muna shanshi acikin gidanmu, innarmu bata cemusu uffan, nikuma mai maida murtanin damuwa ta hanani iya cewa komai, 'yan biki dai zuwa yau kowa yakama gabansa, yanzu dagamu sai mune agidan. Sauk'inmu d'aya tun ranar innaro bata sake shigowa gidanba, inaga baba mai kanwa yahanata. Babu Wanda yay mana maganar komawa makaranta, muma kuma bamuyi yunk'urin zuwanba, kullum dai innarmu NATA k'ok'arin ganin munkwantar da hankalinmu, a koda yaushe cikin mana nasiha take dayimana kwatance da rayuwarta itada mama Rabi'a, takan Nuna mana muhimmancin hak'uri da amfanin yinsa, koda baka ci ribarsa anan gidan duniyaba zakaci ribarsa a lahira inda kowa ke rububin tara ayyukan alkairi. Alhmdllh muma mun fara rage damuwar kodan ganin farin cikinta, Abu d'ayane kecin zukatanmu shine maganar fidda miji da Abbamu yace nayi acikin sati biyu kacal, gashi kuma babu wani tsayayye a hannu. Duk mun rame mun zuge nida munubiya, dama gamunan bawani aukin kirkiba, ahaka muka cinye satin da abin yafaru. Yau ta kasance lahadi, wasu a yaran gidanmu sunata shirin ziyartar gidajen amare, kaf sa'aninmu 'yan matan gidan sunyi shirinsu, Fauziyya, Fiddausi, Safara'u, Haleematu, amma ban da mu, Dan kogaya mana mu shirya ba'ayiba, saima Fauziyya Ce data tashigo da safe gaida innarmu take sanar damu wai mushirya zamuje gidajen amare. Dagani har Munubiya bamuce da ita komaiba, sai 'yar dariya damukayi. Koda suka gama shirinsu basu nememu ba, sai Fauziyya Ce tashigo danta mana magana akan mufito. Turus tayi Dan ganinmu babu wani shiri, hasalima muna falo zaunene, Munubiya ta kwantar da kanta bisa cinyata ina kwance mata kai, innarmu kuma Na zaune gefe suna waya da mama Rabi'a, sai Aiyaan da Aryaan daketa faman buga game. Hira mukeyi da Munubiya akan wasu write-ups datake dubawa a Instagram da akayi akan maganarmu da galadima, cikin damuwa take karanta writeup d'in, shiyyasa bamuga shigiwar Fauziyya ba saida tayi magana... “wai sisters kuna nufin ma ko shiryawa bakuyiba?”. Gaba d'aya muka kalleta, nayi murmushi ina fad'i “kiyi hak'uri Fauziyya, kutafi kawai, har yanzu fita bata kamacemu ba, dan abubuwa basu gama daidaitaba tukunna”. Cikeda damuwa ta gyad'a kai, jiki a sanyaye tace “shikenan saimun dawo”. “ok to Ku gaida mana amare”. Kanta ta jinjina nanama tana ficewa. Munubiya tace, “ALLAH Sarki Fauziyya, itadai tana sonmu”. Nad'an murmusa ina taje mata Wanda Na tsefe, “Munu.... nima ina k'aunar Fauziyya wlhy itada mamansu, sune kad'ai suke sonmu agidannan, Na tabbata wannan fitar dama ba'a sota damuba, itace kawai taketa k'ok'arin taga munje d'in”. “wlhy hakane sweetheart ”. ‘cewar Munubiya’. Innarmu dai tanata waya, Dan haka batace mana komaiba..... ★★★★★★★★★ Lokaci na gabatowa yay shiri yabar hotel d'in, zuwansa airport babu dad'ewa jirginsu yad'aga, sun tsaya a Dubai Abu-dhabi sukayi hutun 1hour sannan suka nufi India. Tunkan jirginsu ya sauka Sauban da Samha sukazo d'aukarsa. Dan haka yana fara taka matakalar jirgin suka hangosa, cikeda jin dad'i suka nufo gareshi. Duk da fuskarsa babu walwala hakan bai hanasu nuna farincikin ganinsa ba, shima dai yayi farin cikin ganinsu, duk da kwanaki 4 kacal kenan da barinsa k'asar. Sauban ya kar6i bag d'in hannunsa yana fad'in yaya welcome”. Kansa ya shafa yana lumshe ido alamun amsawa. Samha ma tace “Wellcom back Uncle Sam”. Ahankali ya furta Thanks you dear, ya school?”. “Alhmdllh Uncle, ya kabaro Nigeria? ”. Murmushi kawai yayi batareda ya amsa mata ba, yasan surutun Samha bamai k'arewa bane, yana amsa wannan wata zata jeho masa. Sauban ya bud'e masa back seat ya zauna, sannan yarufe shi yakoma mazaunin driver, Samha Na gefensa. Idonsa ya lumshe ya maida Kansa ya jingina da kujera. Wani madaidaici Gida suka isa, Wanda baza'a kirashi k'aramiba, sannan ba k'ato baneba, sai dai muce tsaka tsaki. Samha ce tafita da kanta tabud'e gate d'in, Wanda ana ganin komai dake farfajiyar gidan ta jikinsa daga waje. Sauban ya ida shiga da motar, kusada wasu motoci uku yay parking, Samha data k'araso tabud'ema Galadima yafita. Kusan atare suka shiga falon gidan, yana gaba suna baya. Masha ALLAH nafad'a saboda ganin tsaruwar falon, sai dai shiru gidan alamun babu kowa a ciki. Ya zube bisa rukunin kujerun farko dasuka kasance golden color and white. Isaka yad'an turo daga bakinsa sannan ya kalli Sauban dake shirin zama shima. “yanaji gidan shiru? inasu Momma ne?”. “duk suna hospital, har jakadiya ma, zamu tafi d'akko kanema Aunty Mimi tatafi itama, dama ita kad'aice agidan saboda mu muna school ”. “Ok, ya jikin Abie?”. “hummm da sauk'i yaya”. “mik'ewa yayi yana guntun murmushi, tunda yafara girma yafahimci mahaifinsa Na kwance yakejin idan antanbaya Momma jikin Abie tana cewa da sauk'i, amma shi shekaru kusan 25 Abie Na kwance amma shifa baiga wannan sauk'inba, kawai suna dai fad'ane, sauk'i d'ayane zai iya cewa yagani shine magana da idanu da Abie keyi kawai. Da wannan tunanin ya haye steps d'in benen, yana tafiya yana sasaauta tied d'in wuyansa. ahaka harya k'arasa d'akinsa. Komai needs kamar yanda ya barsa, (kullum ne babu fashi sai Samha ta gyara d'akin) Komai a d'akin fari ne, sai golden dasuka kasance d'ai-d'ai. d'akin yayi k'yau sosai, sai tashin k'amshin turarensa daya manne yakeyi, gakuma na air fresheners, saiya had'u yana bada wani ni'im taccen k'amshi. kayansa yashiga cirewa d'ai-d'ai yana sagewa jikin hanger. wanka yashiga sannan ya gabatar da sallan data riskeshi a hanya ......... ★★*★★*★★*★★*★★ Da daddare muna zaune munacin tuwo saiga kiran Abba yashigo wayar innarmu, tana d'agawa yace ta turo masa mu. To kawai tace ya yanke wayar. Kallonmu tayi ad'an sanyaye, tace “idan kun gama cin abincin kuje abbanku Na kira”. Daga ni har Munubiya sai da gabanmu yafad'i, jiki a sanyaye muka amsa da “to innamu”. Kasa cigaba Dacin abincin mukayi, dole muka ajiye kawai mukaje muka wanko hannu..................✍🏼 🤔ko wane kira kuma Abba yakema su Munaya😕?. Barkanmu da dawowa✋🏻, ina fata duk kuna cikin k'oshin lafiya?😄🤝🏻. To gashinan Na k'ara yawan page Masu k'orafi😄⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ *_ya ALLAH ka gafartama iyayenmu_*👏🏻😭 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣3⃣ .......Mun d'anji sanyi a ranmu, ganin kiran bamu kad'ai baneba, hardasu Safara'u Ashe, waje muka samu muka zauna, sannan muka gaidasu. Fiddausi kad'ai ake jira, itama babu jimawa sai gata ta shigo da sallama, duk muka amsa, ta gaida su Abba. Falon yay tsit Na mintuna biyu, sannan Abbanmu yay gyaran murya, kallonmu yake mu duka cikin nazari, ganin muduka mun hallara yace “mun kiraku nan ne saboda dalilin abinda yafaru kwanan nan, hankalina yakasa kwanciya da zamanku a gabanmu, mun yanke shawara nida 'yan uwana zamu aurar daku duka kawai, kowace saita cigaba da karatunta a d'akinta, muma hakan zai sama mana kwanciyar hankali. dan haka kowacce saita sami mai zuwa wajenta ta sanar masa munason ganin magabatansa inhar da gaske yakeyi”. gaba d'aya muka amsa da to abba kanmu ak'asa. Wasunmu murna suke da hakan, amma banda ni da Munubiya, dan bamuda wasu tsayayyu a hannu, bawai samarinne bamu dasuba, a'a wad'anda zamu kawo amatsayin Na aurene matsalarmu. Maganar Dady ce ta katsemin tunani, danaji yana fad'in su sutashi suje, amma ni Na tsaya. Haka suka fice suka barni, duk tsoro yakuma cika zuciyata. bayan fitarsu baba k'arami yanuna min gabansu alamar Na matso. Tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki haka natashi Na isa gabansu, na zauna kaina ak'asa. Baba k'arami yace “Munaya!”. Muryata Na rawa Na amsa da “na'am baba”. Ya gyara zamansa sosai, “Munaya na sanki bak'ya k'arya, kifad'a min tsakaninki da ALLAH miye had'inki da Galadima?”. Gabanane yafad'i daaam!, nai k'ok'arin had'iye kukan daya taho mini “wlhy Baba banida had'in komai dashi, hasalima ban ta6a saninsaba sai awajen hawan sallah, shima ba ganin fuskarsa na ta6a yiba, sai kuma randa mukai karo dashi a filin idi ina neman su kamal, kuma wlhy aranar hak'uri kawai nabashi, koma amsamin baiyiba yatafi, ni banma san shibane alokacin”. “amma miyasa aka buga hotonku kuna cikin plaza d'insa?”. “Dady kuyi hak'uri, tabbas nasan munyi laifi anan, amma Ku yafemin, dan nasan da bamuje plaza d'inba a daren da k'ila hakan bai faruba, amma wlhy abinda yafaru shine...................., cikin nutsuwa ta zayyane musu komai, saidai batace Munubiya ce zata fad'inba, tace itace. Koda basuga ainahin abin da idonsu ba sai zukatansu sukayi sanyi, baba k'arami yace “to ALLAH ya k'yauta, wannan akwai wani Abu daban dabamu saniba acikin lamarin, ALLAH ya warware komai cikin sauk'i”. Duk mukace amin. Dady yace, “Munaya! bisa hak'uri damukaita bama yaya kin sami sassauci akan sati 2 daya ce ki fidda miji, yanzu saiki nutsu ki kawo kamar sauran 'yan uwanki, insha ALLAH bayan babbar salla zamu aurar daku gaba d'aya kawai, ALLAH yayi muku albarka kinji, kucigaba da kare mutuncinku, sannan Ku koma zuwa makaranta tunda abin ya lafa”. Kai na gyad'a sannan nayi godiya. Na iske innarmu da Munubiya jigum-jigum a falo suna jiran dawowata, nasami waje na zauna jikina a sanyaye. Innarmu tace, “miya faru kuma?”. Guntun murmushi nayi INA share kwallar data zubomin, “babu komai innarmu, sun tanbayeni gaskiyar abinda yafaru ne, sannan since sun janye maganar sati biyu nafiddo miji da sukace nayi. nima za'a had'a danawa zuwa bayan salla kamar su Munubiya, kuma since mukoma makaranta”.. Daga Munubiya har innarmu ajiyar zuciya suka sauke, “to Alhmdllhi, ALLAH yabaku mazaje na gari”. ‘cewar innarmu’. A zukatanmu muka amsa mata da amin. Washe gari. Mukayi shirin zuwa makaranta, gudun abinda zaije yadawo sai muka saka nik'af dagani har Munubiya kamar yanda innarmu tabamu shawara muyi. Alhmdllh tunda muka fita bamuci karo da abinda ya Sosa zuciyarmu ba, saboda fuskokinmu arufe suke. A ajima babu Wanda ya shaidamu sai Bilkeesu, nanma dai munyi mun fito lafiya babu wata damuwa. amma saboda a d'ar-d'ar Muke bamu wani sakeba, ana fitowa lectures muka nufi gida. Haka muka cigaba da zuwa makaranta kulum fuska arufe, ko cikin anguwa za'a aikemu saimun saka nik'af, dan yanzu fuskokinmu sunrigada sun zama sannanun fuskoki.... ★★★★★★★★★★ Yana gama kimtsawa yafice, ko abincin da Samha ta shirya nasa bai sauraraba, kai tsaye yanufi Hospital d'i. da Abie ke jinya. da jakadiya yafara cin karo tana rik'e da Khaleel a hannu, khaleel yakwace yataho da gudu yana fad'in “Uncle oyoyo”. Hannayensa ya bud'e masa yafad'a jikinsa, ya shafa kan yaron yana fad'in “my boy ykk?”. “lafiya Uncle Sam... yaushe kadawo?”. Murmushi Galadima yayi, yad'an ja kumatun khaleel “to maganatu yau na dawo”. Dariya yaron yayi, zai sake joho wata maganar Galadima ya d'ora yatsansa akan bakin yaron alamun yayi shiru. Shirun kuwa khaleel yayi dan yasan halin Uncle Sam.. saraii. Jakadiya ta rissina tana gaidashi, amsawa yayi fuskarsa da 'Yar fara'a, ya tambayeta ya jikin Abie. “jiki Alhmdllh ranka ya dad'e”. Kansa kawai ya jinjina mata yay gaba rik'e da hannun Khalel. Da sallama ya shigo d'akin da Abie ke jinya, d'akine babba kamar Bana asibitiba, daka gani Kasan anyisane saboda manyan mutane irinsu, Momma na zauna akujerar gaban gadon da Abie ke kwance, gadon Kansa bawai ainahin gado bane na asibiti, duk wasu na'urori ne ajikinsa, da alama sune suke taimakama jikin Abie d'in, k'umba Momma ke yanke masa. Aunty Mimi na zaune bisa kujerun da aka shirya a gefe tamkar falo, System Ce agabanta tana danne-danne. Sallamar Galadima yasata d'agowa tana murmushi, “My k'ani oyoyo” tafad'a tana ture system d'in daga cinyarta. Murmushi yamata shima, cikin maganarnan tasa ta k'asaita maikama da anmasa tilas yace “my dear aunty barkanki”. Hannu tasa tad'an bigi damtsen hannunsa, cikin wasa tace barka zakace ba bagyka ba”. Shafa Inda tad'an bigesan yakeyi yanda 6ata fuska kamar wani k'aramin yaro, “ALLAH akwai zafi aunty Mimi, wai har yanzu ban girma da buguba awajenki?”. “tab ai da sauranka, sai randa kayi aure zan daina”. Bakinsa ya ta6e yak'arasa inda Momma take yana fad'in, “aiko k'yadad'e baki barinba kenan”. Momma dake murmushi saboda drama d'in tasu ta kalli Abie da shima fuskarsa take a washe alamun yayi farinciki da ganin d'an nasa. Gabansa yaje ya durk'usa, saitin Face d'insa, ya saka hannunsa cikin NASA fuskarsa d'auke da murmushi yace, “my Abie barka da rana”. Da idanu Abie ya amsa masa, dan sune bakin maganar yanzu. Yakuma masa magana da ido alamar yaka barosu?. Murmushi Galadima yayi na takaici, sannan yace, “mai martaba na gaidaka, shima zaizo nextweek”. Farin cikine Yakuma fad'ad'a a fuskar Abie, dasu sukasan yanayinsa, sukad'ai zasu iya fahimtar farin cikinsa ko damuwarsa, musamman ma Momma. Momma dake kallonsu tayi murmushi, Galadima ya maida kallonsa gareta, “Momma na yana sameku?”. “Alhmdllh Muh'd, yaka barosu?”. Baki yad'an ta6e sannan yace “lfy lau, ya jikin Abie?”. “jiki Alhmdllhi, dan randa ka tafi yatsun hannun damarsa sund'an motsa”. Da Sauri Galadima yace “da gaske Momma?” yay maganarne yana kallon hannun Abie d'in, sannan cikeda farin cikin ya sumbaci hannun yana fad'in Alhmdllh ala kulli halin, ALLAH yabaka lafiya my sweet Abie”. Lumshe idanu Abie yayi farinciki na k'ara fad'ad'a a face nashi, aunty Mimi da momma da jakadiya suna kallonsu cikeda tausayi suka amsa da amin. khalel yata6a kafad'arsa, juyowa yayi yana kallonsa. yaron yakai hannu yana sharema Galadima hawayen dasuke kwance a kumatunsa. galadima yajawosa ya rungume yana sumbatar kan yaron, fuskarsa d'auke da murmushi. ★★★ Yau mune k'arshen tafiya school, saboda lectures d'in yamma ne damu, Fauziyya kuma batada lafiya bazatajeba. Kasancewar abubuwa sun kuma lafawa yau sai bamu saka nik'af ba, amma yana rik'e a hannunmu idan mun shiga cshool zamu saka. Mun fito bakin titi muna jiran taxi ko napep saiga wata bak'ar mota wulik ta faka agabanmu, dagani har Munubiya d'auke kanmu mukayi gefe. Mai motar ya sauke glass d'in yana kallonmu, sallama yayi mana, Munubiya ta amsa, nikam koma kallo bai isheniba. Ganin haka saiya bud'e motar yafito, matashin saurayine bak'i k'yak'yk'yawa mai yawan fara'a. Yace, “haba 'yan mata, babu fad'a miya kawo gaba”. Cikeda tsiwa nace “sai aka cemaka mu 'yan matane? to matan aurene”. Murmushi yayi, sannan ya gyara tsayuwarsa, “dear hakan ma dakikayi yakuma tabbatar min da Bahaka baneba”. d'an hararsa nayi na d'auke kaina, danni yanzu maza duk haushi suke bani wlhy. Dariya yayi, “oh sweety karkisa na sume mikifa a titinnan”. Ganin yana neman shiga hancinmu yasani jan hannun Munubiya muka bar wajen, k'yalemu yayi Yakoma mota ya zauna. har muka sami abin hawa yana kallonmu. haka yayta bin mai napep d'in har k'ofar makaranta, daga nan kuma bamusan ya akayiba mudai muka shige. Kwana biyu da faruwar haka muna wanki a tsakar gida saiga ya Anas yashigo, ya kallemu yana murmushi, twins cikinku waye mai saurayi mai bak'ar mota?”. Mu duka kallonsa mukayi, gwaggon Haleema da maman safara'u dake aiki a tsakar gidan suma duk suka kallemu. Da sauri Munubiya tace “munaya Ce yaa Anas”. “kije to yana jiranki a k'ofar gida”. harara na dallama Munubiya “wlhy Munubiya k'arya dai babu k'yau”. Dariya tayi tacigaba da wankinta, “kitashi kije kina 6ata masa lokaci”. Hijjab na d'auka nafita danufin zuwa na sauke masa masifa na dawo. Gwaggon Haleematu da maman Safara'u suka bini da kallo cikin wani yanayi. oho ni bammasan sunayiba. Jingine da motarsa na gansa, sanye yake da shadda ruwan zuma, harda hula, sa6anin ranar damuka gansa da k'ananun kaya, kwarjini yamin nakasa masa masifar danayi niyya, namasa sallama sannan nace “miya kawoka k'ofar gidanmu? waya nuna maka ma?”. Yad'an murmusa, “miyake kawo saurayi gidansu budurwa?”. “oho maka” Nafad'a cikin kauda kai gefe. “kimga baby sorry, mu ajiye wannan drama d'in, ni bada wasa Nazo nanba, tun randa na ganku keda 'yar uwarki kuka rikatani, nasa a raina duk wadda ALLAH yabani cikinku tamin, bansami kwanciyar hankaliba saida na binciko gidanku, sunana Haidar Mustapha”. Shiru nayi ban tanka masaba. Yay murmushi yana matsowa kusa dani, “please mana baby, kimin magana?”. Da k'yar ya sami na amsashi sannan nima nafad'a masa nawa sunan. abinda na fuskanta da haidar shi mutumne mai sauk'in kai, sannan ko kad'an banga alamun yaudara ba tattare dashi. Cikin kwanaki kad'an mungama sabawa da haidar, sabawa maiban mamaki, wadda nikaina har mamakin kaina nakeyi wlhy. Alokacinne kuma yaa Marwan shima ya nuna yanason Munubiya, wayyo zokuga farin ciki wajen iyayenmu, tamkar su zuba ruwa a k'asa susha dan dad'i. Wannan Abu fa ya bak'anta ran 'yan gidanmu, sunso ace munyi kwantai, har agama sakama 'ya'yansu rana mu babu mazaje a hannu, amma ALLAH ya fisu ai. Kud'in Munubiya aka fara kawowa gidanmu, daga nan saina Safara'u. nima saiga iyayen Haidar sunzo, ranar har kukan dad'i mukayi muda innarmu, duk wani masoyinmu zai tayamu murna akan wannan al'amari, dan ba'a ta6a tunanin zamu iya samun mazaje da wuri ba saboda abinda yafaru. Sauran 'yan uwanmu ma duk ankawo kud'ad'en aurensu, dandanan aka tsaida ranar aure, watanni uku kacal, bayan salla babba da wata biyu. Zuwa yanzu kam hankalinmu ya kwanta, sai dai matsaloli na gidanmu da basa k'arewa, saikuma abinda yafaru tsakaninmu da Galadima, wani lokacin mukan fuskanci tozarci daga wasu jama'a idan mun fita, tunma muna zama muyi kuka har zukatanmu suka fara dakewa. Galadima kam bamu sake koda jin d'uriyar saba, hakama Fu'aad, tunima Haidar ya mantar dani wani Fu'aad gaba d'aya. Ahaka babbar Salla tafara gabatowa. Masu shiri natayi, nikam dai babu mu aciki, dagani har Munubiya munyi alk'awarin babu inda zamuje sai gidan mama Rabi'a........ Munshiga bikin salla lafiya, inda iyayenmu sukayi layya kamar yanda kowacce shekara suka saba, itama innaro anmata, babu inda mukaje wannan karon, su Safara'u dai ansha yawo, ranar suyar nama kuma saiga dukkanin amare sunzo yawon salla, abin tamkar had'in baki, kowaccensu tayi 6ul-6ul da ita, harma damasu tsarabar ciki. Kowacce jinta take a sama, mijinta yafi na kowa, iyayensu kam anata baza hak'wara da tink'aho ana zuba mana habaici. Babu Wanda ya tanka musu acikinmu, dan innarmu ta hana. wajen Ayusher mukejin wai babu Galadima a hawan salla wannan karon, hakan bai dameniba, danni baya gabana, nama manta dawani Galadima can. Bayan gama bikin salla da kwanaki uku saiga wani tashin hankali. Iyayen Haidar sunzo wai abasu kayansu sun fasa, ance musu ni 'Yar iskace. Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Yau munga tashin hankali muda innarmu, kuka da hawaye innarmu keyi itada mama Rabi'a, haka aka had'a kayansu aka basu. Innaro tashigo tafara tata tsiya babuji babu gani, sai zuba cin mutunci takeyi ga innarmu, 'yan gidanmu natajin dad'i, jisuke kamar anmusu gafara da fasa aurennan nawa, aganinsu yaza'ayi 'ya'yansu suna auren masu kud'i nima na auri mai kud'i, ai bazai yuwuba.. Cikin kuka nakira Haidar ina tanbayarsa miyasa zaimin haka, yasan tun farko ba sona yakeba miyasa yazo gidanmu har iyayensa suka shiga. “k dalla malama yimin shiru, ni mahaukacine zan auri yarinyar da aka buga hotonta jikin jarida wani na kissing d'inta, ok da an 6oyemin za'a bani sauran wani Ashe ked'in karuwar Galadima ce, to ALLAH ya toni asirinku dagake har iyayen naki, ko a hanya muka had'u karki kuma nuna kin sanni ma”. Baki na bud'e da nufin maida masa murtani ya yanke wayar, nayi saurin kuma kira amma sai najita arufe. Kuka na fashe dashi, bansan miya faruba sai dai najini ak'asa kawai. Cikeda tashin hankali Munubiya tayo kaina tana kuka da girgizani. Dandanan d'akin yacika dasu Dady, babu alamar rai atare dani, hakan yasa aka d'aukeni da gaggawa sai asibiti......... ★★★★★ A 6angaren Galadima kuwa wasu ayyukane suka d'auke hankalinsa, gaba d'aya yayi busy saboda kamfaninsu na k'ok'arin fidda wata waya sabuwar k'ira. Abinda ya faru kuwa a Nigeria ya watsar dashi gefe, saboda gargad'in da doctor d'insa yamasa akan yarage yawan damuwa, saboda ciwonsa yana k'ok'arin tashi. Haka yadage yacire komai d'in, amma har yanzu yasaka amasa aikin bincike ta k'ark'ashin k'asa, sannan iyalan manager sun ku6uta suma, yabar Nigeria da sati biyu suka sakosu. Gaba d'aya ya ajiye duk wani abinda yashafi Nigeria a gefe, ko bikin salla bai hakarta ba, sannan zuwan dayankan yi duk karshen wata ma ya daina, Momma batace dashi komaiba akan k'in zuwan nasa. Dan lokacin da mai martaba (mahaifin momma) yazo sun tattauna sosai akan abinda yafaru, shine yace Galadima yad'an tsahirta da zuwa Nigeria nawani lokaci, idan komai ya lafa sai acigaba da bincike, dan wad'anda suka aikata sumafa baza suyi barciba, yanzu idonsu abud'e yake akan komai, amma idan anyi burus dasu komai ya lafa sai a d'auki mataki. Wannan yasa bai sake zuwaba, gameda business d'insa nacan kuwa Harun yana tsaye akan komai. Fitowarsa kenan daga office zaije gida yad'an kimtsa sannan yaje asibi, wayarsa tashi ruri, zarota yayi daga aljihu ya duba, ganin Muftahu a kan layi saiya maida wayar cikin aljihu kawai batare da ya amsaba. Hannu yabama beejay abokin aikinsa sukayi sallama akan saikuma gobe. yana k'ok'arin shiga motar kiran yakuma shigowa, shiga yayi ya zauna sannan ya d'aga, suka gaisa da Muftahu, ya tambayesa jikin Abie. Shikuma ya amsa da Alhmdllh. Muftahu yace, “ALLAH yasa ban takuraka ba? Inason muyi magana ne dama”. Kwantar da kansa yayi jikin kujera ya lumshe idanunsa, cikeda k'asaita ya furta “ina saurarenka”. Daga can Muftahu yay murmushi, sannan yace “dama akan yarannan ne, d'aya daga cikinsu an fasa aurenta, wai Wanda zai auretan yace yafasa sabo...da sa... sa.... yakasa fad'a saboda maganar tamasa nauyi abaki” Galadina yace “kafad'a mana, kasanfa bana son kwana-kwana a magana ni”. “wlhy maganarce babu dad'in ji, ca yayfa wai ita karuwarka ce, yanzu haka yarinyar tana asibitima”. Da k'arfi ya cije lips d'insa, zuciyarsa na suya, saikuma ya saki guntun murmushin takaci, yatashi zaune yana bud'e idonsa, “humm Muftahu waye shi yaron dazata aura d'in?”. “wlhy ban saniba nima”. “o right karka damu, zanyi tunani akan lamarin, ni bamma duba bayanai daka turomin akan yarinyarba fa, abubuwa sunmun yawane wlhy. amma masu bibiyar tata basuga wani abunda ya shafi waccan maganarba?”. “Gaskiya basuga wani abuba sa6anin tunaninmu, ammafa bama yarinya d'aya bace ba, twins ne, kaduba bayanan kagani”. “ok sai munyi magana kenan”. Bayan sunyi sallama yay shiru yana tunani a ransa, da gani kasan ransa a6ace yake, ya furzar da huci daga bakinsa sannan ya tada motar yatafi. idonsa yayi jajir saboda bak'in ciki, yanzun har takai wani yafasa auren wata akansa? waye yamasa wannan abin? miya masa ne da zafi haka ya tozartashi? wlhy yayi alk'awarin duk Wanda keda hannu akan wannan tozarcin da akai masa bazai d'aga masa k'afaba, dolene yayi dana sanin saninsa. Da wannan tunanin ya k'arasa gida. Babu kowa a gidan sai jakadiya, su Sauban suna makaranta, Aunty Mimi da Momma kuma suna asibiti, jakadiya ta rissina tana gaidashi, hannu kawai ya iya d'aga mata ya haye sama. Binsa tayi da kallon tausayi, hakan da yayi mata ya nuna ransa a 6ace yake, danshi mutum ne mai girmama nagaba dashi, dukda tana a k'ark'ashinsu bai ta6a wulak'antata ba, wannan tarbiyar mahaifiyarsu ce kuma. Koda yashiga rigarsa kawai yacire ya zauna a bakin gado, medical glasses d'insa yasaka sannan yajawo System yabud'e, Emailil na Muftahu ya shiga. Dukkan bayanai da tarihin su Munaya ne awajen. Gaba d'aya ya nutsu ga abinda yake karantawar, shi mamakima abin yabashi, sukuma wane irin gida wad'annan yaran suka fito haka? Wani abun yakan bashi dariya (sai dai yakanyi dariyar ne a zuciyarsa), wani kuma haushi, tsaf yagama karanta tarihin yaran masu kama da juna. Ya mik'e yana zagaye d'akin da tunanin miye mafita, har yanzu zuciyarsa bata bar karanta masa da hannun wad'an yaran aka masa wannan abunba, sai dai shi kansa yana tambayar kanasa mizaisa su aikata? miye kuma ribarsu bayan suma hardasu aka tozarta?. yanzu kuma zuciyarsa na masa wani tunani daban bayan yaji tarihinsu. Zuciyarsa na cigaba da tunzurashi akan yayi amfani da damar k'arshe wajen bincikensa, tunda yabi dukkanin sauran bai samu wani bakin zareba. To amma kuma wannan ai ba tarbiyyar Malam bahaushe baceba, daga baya kuma idan komai yafitofa? wane kallo kuma za'a masa?, shinma zata iya fahimtarsa kuwa? dan irin wannan abun yakan farune a labaran films ko Novels, to amma wannan ce damarsa ta k'arshe ai kawai, dolene ya jefi tsuntsu biyu da dutsi d'aya kenan?.............✍🏼 Tirk'ashi, Nikam dai nakasa fahimtar wannan cirkud'ad'd'en tunanin na Galadima☹, fan's koku kun fahimta Ku fassara mana🤔?. *_Ya ALLAH ka gafartama iyayenmu😭👏🏻_* *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣3⃣ .......Mun d'anji sanyi a ranmu, ganin kiran bamu kad'ai baneba, hardasu Safara'u Ashe, waje muka samu muka zauna, sannan muka gaidasu. Fiddausi kad'ai ake jira, itama babu jimawa sai gata ta shigo da sallama, duk muka amsa, ta gaida su Abba. Falon yay tsit Na mintuna biyu, sannan Abbanmu yay gyaran murya, kallonmu yake mu duka cikin nazari, ganin muduka mun hallara yace “mun kiraku nan ne saboda dalilin abinda yafaru kwanan nan, hankalina yakasa kwanciya da zamanku a gabanmu, mun yanke shawara nida 'yan uwana zamu aurar daku duka kawai, kowace saita cigaba da karatunta a d'akinta, muma hakan zai sama mana kwanciyar hankali. dan haka kowacce saita sami mai zuwa wajenta ta sanar masa munason ganin magabatansa inhar da gaske yakeyi”. gaba d'aya muka amsa da to abba kanmu ak'asa. Wasunmu murna suke da hakan, amma banda ni da Munubiya, dan bamuda wasu tsayayyu a hannu, bawai samarinne bamu dasuba, a'a wad'anda zamu kawo amatsayin Na aurene matsalarmu. Maganar Dady ce ta katsemin tunani, danaji yana fad'in su sutashi suje, amma ni Na tsaya. Haka suka fice suka barni, duk tsoro yakuma cika zuciyata. bayan fitarsu baba k'arami yanuna min gabansu alamar Na matso. Tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki haka natashi Na isa gabansu, na zauna kaina ak'asa. Baba k'arami yace “Munaya!”. Muryata Na rawa Na amsa da “na'am baba”. Ya gyara zamansa sosai, “Munaya na sanki bak'ya k'arya, kifad'a min tsakaninki da ALLAH miye had'inki da Galadima?”. Gabanane yafad'i daaam!, nai k'ok'arin had'iye kukan daya taho mini “wlhy Baba banida had'in komai dashi, hasalima ban ta6a saninsaba sai awajen hawan sallah, shima ba ganin fuskarsa na ta6a yiba, sai kuma randa mukai karo dashi a filin idi ina neman su kamal, kuma wlhy aranar hak'uri kawai nabashi, koma amsamin baiyiba yatafi, ni banma san shibane alokacin”. “amma miyasa aka buga hotonku kuna cikin plaza d'insa?”. “Dady kuyi hak'uri, tabbas nasan munyi laifi anan, amma Ku yafemin, dan nasan da bamuje plaza d'inba a daren da k'ila hakan bai faruba, amma wlhy abinda yafaru shine...................., cikin nutsuwa ta zayyane musu komai, saidai batace Munubiya ce zata fad'inba, tace itace. Koda basuga ainahin abin da idonsu ba sai zukatansu sukayi sanyi, baba k'arami yace “to ALLAH ya k'yauta, wannan akwai wani Abu daban dabamu saniba acikin lamarin, ALLAH ya warware komai cikin sauk'i”. Duk mukace amin. Dady yace, “Munaya! bisa hak'uri damukaita bama yaya kin sami sassauci akan sati 2 daya ce ki fidda miji, yanzu saiki nutsu ki kawo kamar sauran 'yan uwanki, insha ALLAH bayan babbar salla zamu aurar daku gaba d'aya kawai, ALLAH yayi muku albarka kinji, kucigaba da kare mutuncinku, sannan Ku koma zuwa makaranta tunda abin ya lafa”. Kai na gyad'a sannan nayi godiya. Na iske innarmu da Munubiya jigum-jigum a falo suna jiran dawowata, nasami waje na zauna jikina a sanyaye. Innarmu tace, “miya faru kuma?”. Guntun murmushi nayi INA share kwallar data zubomin, “babu komai innarmu, sun tanbayeni gaskiyar abinda yafaru ne, sannan since sun janye maganar sati biyu nafiddo miji da sukace nayi. nima za'a had'a danawa zuwa bayan salla kamar su Munubiya, kuma since mukoma makaranta”.. Daga Munubiya har innarmu ajiyar zuciya suka sauke, “to Alhmdllhi, ALLAH yabaku mazaje na gari”. ‘cewar innarmu’. A zukatanmu muka amsa mata da amin. Washe gari. Mukayi shirin zuwa makaranta, gudun abinda zaije yadawo sai muka saka nik'af dagani har Munubiya kamar yanda innarmu tabamu shawara muyi. Alhmdllh tunda muka fita bamuci karo da abinda ya Sosa zuciyarmu ba, saboda fuskokinmu arufe suke. A ajima babu Wanda ya shaidamu sai Bilkeesu, nanma dai munyi mun fito lafiya babu wata damuwa. amma saboda a d'ar-d'ar Muke bamu wani sakeba, ana fitowa lectures muka nufi gida. Haka muka cigaba da zuwa makaranta kulum fuska arufe, ko cikin anguwa za'a aikemu saimun saka nik'af, dan yanzu fuskokinmu sunrigada sun zama sannanun fuskoki.... ★★★★★★★★★★ Yana gama kimtsawa yafice, ko abincin da Samha ta shirya nasa bai sauraraba, kai tsaye yanufi Hospital d'i. da Abie ke jinya. da jakadiya yafara cin karo tana rik'e da Khaleel a hannu, khaleel yakwace yataho da gudu yana fad'in “Uncle oyoyo”. Hannayensa ya bud'e masa yafad'a jikinsa, ya shafa kan yaron yana fad'in “my boy ykk?”. “lafiya Uncle Sam... yaushe kadawo?”. Murmushi Galadima yayi, yad'an ja kumatun khaleel “to maganatu yau na dawo”. Dariya yaron yayi, zai sake joho wata maganar Galadima ya d'ora yatsansa akan bakin yaron alamun yayi shiru. Shirun kuwa khaleel yayi dan yasan halin Uncle Sam.. saraii. Jakadiya ta rissina tana gaidashi, amsawa yayi fuskarsa da 'Yar fara'a, ya tambayeta ya jikin Abie. “jiki Alhmdllh ranka ya dad'e”. Kansa kawai ya jinjina mata yay gaba rik'e da hannun Khalel. Da sallama ya shigo d'akin da Abie ke jinya, d'akine babba kamar Bana asibitiba, daka gani Kasan anyisane saboda manyan mutane irinsu, Momma na zauna akujerar gaban gadon da Abie ke kwance, gadon Kansa bawai ainahin gado bane na asibiti, duk wasu na'urori ne ajikinsa, da alama sune suke taimakama jikin Abie d'in, k'umba Momma ke yanke masa. Aunty Mimi na zaune bisa kujerun da aka shirya a gefe tamkar falo, System Ce agabanta tana danne-danne. Sallamar Galadima yasata d'agowa tana murmushi, “My k'ani oyoyo” tafad'a tana ture system d'in daga cinyarta. Murmushi yamata shima, cikin maganarnan tasa ta k'asaita maikama da anmasa tilas yace “my dear aunty barkanki”. Hannu tasa tad'an bigi damtsen hannunsa, cikin wasa tace barka zakace ba bagyka ba”. Shafa Inda tad'an bigesan yakeyi yanda 6ata fuska kamar wani k'aramin yaro, “ALLAH akwai zafi aunty Mimi, wai har yanzu ban girma da buguba awajenki?”. “tab ai da sauranka, sai randa kayi aure zan daina”. Bakinsa ya ta6e yak'arasa inda Momma take yana fad'in, “aiko k'yadad'e baki barinba kenan”. Momma dake murmushi saboda drama d'in tasu ta kalli Abie da shima fuskarsa take a washe alamun yayi farinciki da ganin d'an nasa. Gabansa yaje ya durk'usa, saitin Face d'insa, ya saka hannunsa cikin NASA fuskarsa d'auke da murmushi yace, “my Abie barka da rana”. Da idanu Abie ya amsa masa, dan sune bakin maganar yanzu. Yakuma masa magana da ido alamar yaka barosu?. Murmushi Galadima yayi na takaici, sannan yace, “mai martaba na gaidaka, shima zaizo nextweek”. Farin cikine Yakuma fad'ad'a a fuskar Abie, dasu sukasan yanayinsa, sukad'ai zasu iya fahimtar farin cikinsa ko damuwarsa, musamman ma Momma. Momma dake kallonsu tayi murmushi, Galadima ya maida kallonsa gareta, “Momma na yana sameku?”. “Alhmdllh Muh'd, yaka barosu?”. Baki yad'an ta6e sannan yace “lfy lau, ya jikin Abie?”. “jiki Alhmdllhi, dan randa ka tafi yatsun hannun damarsa sund'an motsa”. Da Sauri Galadima yace “da gaske Momma?” yay maganarne yana kallon hannun Abie d'in, sannan cikeda farin cikin ya sumbaci hannun yana fad'in Alhmdllh ala kulli halin, ALLAH yabaka lafiya my sweet Abie”. Lumshe idanu Abie yayi farinciki na k'ara fad'ad'a a face nashi, aunty Mimi da momma da jakadiya suna kallonsu cikeda tausayi suka amsa da amin. khalel yata6a kafad'arsa, juyowa yayi yana kallonsa. yaron yakai hannu yana sharema Galadima hawayen dasuke kwance a kumatunsa. galadima yajawosa ya rungume yana sumbatar kan yaron, fuskarsa d'auke da murmushi. ★★★ Yau mune k'arshen tafiya school, saboda lectures d'in yamma ne damu, Fauziyya kuma batada lafiya bazatajeba. Kasancewar abubuwa sun kuma lafawa yau sai bamu saka nik'af ba, amma yana rik'e a hannunmu idan mun shiga cshool zamu saka. Mun fito bakin titi muna jiran taxi ko napep saiga wata bak'ar mota wulik ta faka agabanmu, dagani har Munubiya d'auke kanmu mukayi gefe. Mai motar ya sauke glass d'in yana kallonmu, sallama yayi mana, Munubiya ta amsa, nikam koma kallo bai isheniba. Ganin haka saiya bud'e motar yafito, matashin saurayine bak'i k'yak'yk'yawa mai yawan fara'a. Yace, “haba 'yan mata, babu fad'a miya kawo gaba”. Cikeda tsiwa nace “sai aka cemaka mu 'yan matane? to matan aurene”. Murmushi yayi, sannan ya gyara tsayuwarsa, “dear hakan ma dakikayi yakuma tabbatar min da Bahaka baneba”. d'an hararsa nayi na d'auke kaina, danni yanzu maza duk haushi suke bani wlhy. Dariya yayi, “oh sweety karkisa na sume mikifa a titinnan”. Ganin yana neman shiga hancinmu yasani jan hannun Munubiya muka bar wajen, k'yalemu yayi Yakoma mota ya zauna. har muka sami abin hawa yana kallonmu. haka yayta bin mai napep d'in har k'ofar makaranta, daga nan kuma bamusan ya akayiba mudai muka shige. Kwana biyu da faruwar haka muna wanki a tsakar gida saiga ya Anas yashigo, ya kallemu yana murmushi, twins cikinku waye mai saurayi mai bak'ar mota?”. Mu duka kallonsa mukayi, gwaggon Haleema da maman safara'u dake aiki a tsakar gidan suma duk suka kallemu. Da sauri Munubiya tace “munaya Ce yaa Anas”. “kije to yana jiranki a k'ofar gida”. harara na dallama Munubiya “wlhy Munubiya k'arya dai babu k'yau”. Dariya tayi tacigaba da wankinta, “kitashi kije kina 6ata masa lokaci”. Hijjab na d'auka nafita danufin zuwa na sauke masa masifa na dawo. Gwaggon Haleematu da maman Safara'u suka bini da kallo cikin wani yanayi. oho ni bammasan sunayiba. Jingine da motarsa na gansa, sanye yake da shadda ruwan zuma, harda hula, sa6anin ranar damuka gansa da k'ananun kaya, kwarjini yamin nakasa masa masifar danayi niyya, namasa sallama sannan nace “miya kawoka k'ofar gidanmu? waya nuna maka ma?”. Yad'an murmusa, “miyake kawo saurayi gidansu budurwa?”. “oho maka” Nafad'a cikin kauda kai gefe. “kimga baby sorry, mu ajiye wannan drama d'in, ni bada wasa Nazo nanba, tun randa na ganku keda 'yar uwarki kuka rikatani, nasa a raina duk wadda ALLAH yabani cikinku tamin, bansami kwanciyar hankaliba saida na binciko gidanku, sunana Haidar Mustapha”. Shiru nayi ban tanka masaba. Yay murmushi yana matsowa kusa dani, “please mana baby, kimin magana?”. Da k'yar ya sami na amsashi sannan nima nafad'a masa nawa sunan. abinda na fuskanta da haidar shi mutumne mai sauk'in kai, sannan ko kad'an banga alamun yaudara ba tattare dashi. Cikin kwanaki kad'an mungama sabawa da haidar, sabawa maiban mamaki, wadda nikaina har mamakin kaina nakeyi wlhy. Alokacinne kuma yaa Marwan shima ya nuna yanason Munubiya, wayyo zokuga farin ciki wajen iyayenmu, tamkar su zuba ruwa a k'asa susha dan dad'i. Wannan Abu fa ya bak'anta ran 'yan gidanmu, sunso ace munyi kwantai, har agama sakama 'ya'yansu rana mu babu mazaje a hannu, amma ALLAH ya fisu ai. Kud'in Munubiya aka fara kawowa gidanmu, daga nan saina Safara'u. nima saiga iyayen Haidar sunzo, ranar har kukan dad'i mukayi muda innarmu, duk wani masoyinmu zai tayamu murna akan wannan al'amari, dan ba'a ta6a tunanin zamu iya samun mazaje da wuri ba saboda abinda yafaru. Sauran 'yan uwanmu ma duk ankawo kud'ad'en aurensu, dandanan aka tsaida ranar aure, watanni uku kacal, bayan salla babba da wata biyu. Zuwa yanzu kam hankalinmu ya kwanta, sai dai matsaloli na gidanmu da basa k'arewa, saikuma abinda yafaru tsakaninmu da Galadima, wani lokacin mukan fuskanci tozarci daga wasu jama'a idan mun fita, tunma muna zama muyi kuka har zukatanmu suka fara dakewa. Galadima kam bamu sake koda jin d'uriyar saba, hakama Fu'aad, tunima Haidar ya mantar dani wani Fu'aad gaba d'aya. Ahaka babbar Salla tafara gabatowa. Masu shiri natayi, nikam dai babu mu aciki, dagani har Munubiya munyi alk'awarin babu inda zamuje sai gidan mama Rabi'a........ Munshiga bikin salla lafiya, inda iyayenmu sukayi layya kamar yanda kowacce shekara suka saba, itama innaro anmata, babu inda mukaje wannan karon, su Safara'u dai ansha yawo, ranar suyar nama kuma saiga dukkanin amare sunzo yawon salla, abin tamkar had'in baki, kowaccensu tayi 6ul-6ul da ita, harma damasu tsarabar ciki. Kowacce jinta take a sama, mijinta yafi na kowa, iyayensu kam anata baza hak'wara da tink'aho ana zuba mana habaici. Babu Wanda ya tanka musu acikinmu, dan innarmu ta hana. wajen Ayusher mukejin wai babu Galadima a hawan salla wannan karon, hakan bai dameniba, danni baya gabana, nama manta dawani Galadima can. Bayan gama bikin salla da kwanaki uku saiga wani tashin hankali. Iyayen Haidar sunzo wai abasu kayansu sun fasa, ance musu ni 'Yar iskace. Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Yau munga tashin hankali muda innarmu, kuka da hawaye innarmu keyi itada mama Rabi'a, haka aka had'a kayansu aka basu. Innaro tashigo tafara tata tsiya babuji babu gani, sai zuba cin mutunci takeyi ga innarmu, 'yan gidanmu natajin dad'i, jisuke kamar anmusu gafara da fasa aurennan nawa, aganinsu yaza'ayi 'ya'yansu suna auren masu kud'i nima na auri mai kud'i, ai bazai yuwuba.. Cikin kuka nakira Haidar ina tanbayarsa miyasa zaimin haka, yasan tun farko ba sona yakeba miyasa yazo gidanmu har iyayensa suka shiga. “k dalla malama yimin shiru, ni mahaukacine zan auri yarinyar da aka buga hotonta jikin jarida wani na kissing d'inta, ok da an 6oyemin za'a bani sauran wani Ashe ked'in karuwar Galadima ce, to ALLAH ya toni asirinku dagake har iyayen naki, ko a hanya muka had'u karki kuma nuna kin sanni ma”. Baki na bud'e da nufin maida masa murtani ya yanke wayar, nayi saurin kuma kira amma sai najita arufe. Kuka na fashe dashi, bansan miya faruba sai dai najini ak'asa kawai. Cikeda tashin hankali Munubiya tayo kaina tana kuka da girgizani. Dandanan d'akin yacika dasu Dady, babu alamar rai atare dani, hakan yasa aka d'aukeni da gaggawa sai asibiti......... ★★★★★ A 6angaren Galadima kuwa wasu ayyukane suka d'auke hankalinsa, gaba d'aya yayi busy saboda kamfaninsu na k'ok'arin fidda wata waya sabuwar k'ira. Abinda ya faru kuwa a Nigeria ya watsar dashi gefe, saboda gargad'in da doctor d'insa yamasa akan yarage yawan damuwa, saboda ciwonsa yana k'ok'arin tashi. Haka yadage yacire komai d'in, amma har yanzu yasaka amasa aikin bincike ta k'ark'ashin k'asa, sannan iyalan manager sun ku6uta suma, yabar Nigeria da sati biyu suka sakosu. Gaba d'aya ya ajiye duk wani abinda yashafi Nigeria a gefe, ko bikin salla bai hakarta ba, sannan zuwan dayankan yi duk karshen wata ma ya daina, Momma batace dashi komaiba akan k'in zuwan nasa. Dan lokacin da mai martaba (mahaifin momma) yazo sun tattauna sosai akan abinda yafaru, shine yace Galadima yad'an tsahirta da zuwa Nigeria nawani lokaci, idan komai ya lafa sai acigaba da bincike, dan wad'anda suka aikata sumafa baza suyi barciba, yanzu idonsu abud'e yake akan komai, amma idan anyi burus dasu komai ya lafa sai a d'auki mataki. Wannan yasa bai sake zuwaba, gameda business d'insa nacan kuwa Harun yana tsaye akan komai. Fitowarsa kenan daga office zaije gida yad'an kimtsa sannan yaje asibi, wayarsa tashi ruri, zarota yayi daga aljihu ya duba, ganin Muftahu a kan layi saiya maida wayar cikin aljihu kawai batare da ya amsaba. Hannu yabama beejay abokin aikinsa sukayi sallama akan saikuma gobe. yana k'ok'arin shiga motar kiran yakuma shigowa, shiga yayi ya zauna sannan ya d'aga, suka gaisa da Muftahu, ya tambayesa jikin Abie. Shikuma ya amsa da Alhmdllh. Muftahu yace, “ALLAH yasa ban takuraka ba? Inason muyi magana ne dama”. Kwantar da kansa yayi jikin kujera ya lumshe idanunsa, cikeda k'asaita ya furta “ina saurarenka”. Daga can Muftahu yay murmushi, sannan yace “dama akan yarannan ne, d'aya daga cikinsu an fasa aurenta, wai Wanda zai auretan yace yafasa sabo...da sa... sa.... yakasa fad'a saboda maganar tamasa nauyi abaki” Galadina yace “kafad'a mana, kasanfa bana son kwana-kwana a magana ni”. “wlhy maganarce babu dad'in ji, ca yayfa wai ita karuwarka ce, yanzu haka yarinyar tana asibitima”. Da k'arfi ya cije lips d'insa, zuciyarsa na suya, saikuma ya saki guntun murmushin takaci, yatashi zaune yana bud'e idonsa, “humm Muftahu waye shi yaron dazata aura d'in?”. “wlhy ban saniba nima”. “o right karka damu, zanyi tunani akan lamarin, ni bamma duba bayanai daka turomin akan yarinyarba fa, abubuwa sunmun yawane wlhy. amma masu bibiyar tata basuga wani abunda ya shafi waccan maganarba?”. “Gaskiya basuga wani abuba sa6anin tunaninmu, ammafa bama yarinya d'aya bace ba, twins ne, kaduba bayanan kagani”. “ok sai munyi magana kenan”. Bayan sunyi sallama yay shiru yana tunani a ransa, da gani kasan ransa a6ace yake, ya furzar da huci daga bakinsa sannan ya tada motar yatafi. idonsa yayi jajir saboda bak'in ciki, yanzun har takai wani yafasa auren wata akansa? waye yamasa wannan abin? miya masa ne da zafi haka ya tozartashi? wlhy yayi alk'awarin duk Wanda keda hannu akan wannan tozarcin da akai masa bazai d'aga masa k'afaba, dolene yayi dana sanin saninsa. Da wannan tunanin ya k'arasa gida. Babu kowa a gidan sai jakadiya, su Sauban suna makaranta, Aunty Mimi da Momma kuma suna asibiti, jakadiya ta rissina tana gaidashi, hannu kawai ya iya d'aga mata ya haye sama. Binsa tayi da kallon tausayi, hakan da yayi mata ya nuna ransa a 6ace yake, danshi mutum ne mai girmama nagaba dashi, dukda tana a k'ark'ashinsu bai ta6a wulak'antata ba, wannan tarbiyar mahaifiyarsu ce kuma. Koda yashiga rigarsa kawai yacire ya zauna a bakin gado, medical glasses d'insa yasaka sannan yajawo System yabud'e, Emailil na Muftahu ya shiga. Dukkan bayanai da tarihin su Munaya ne awajen. Gaba d'aya ya nutsu ga abinda yake karantawar, shi mamakima abin yabashi, sukuma wane irin gida wad'annan yaran suka fito haka? Wani abun yakan bashi dariya (sai dai yakanyi dariyar ne a zuciyarsa), wani kuma haushi, tsaf yagama karanta tarihin yaran masu kama da juna. Ya mik'e yana zagaye d'akin da tunanin miye mafita, har yanzu zuciyarsa bata bar karanta masa da hannun wad'an yaran aka masa wannan abunba, sai dai shi kansa yana tambayar kanasa mizaisa su aikata? miye kuma ribarsu bayan suma hardasu aka tozarta?. yanzu kuma zuciyarsa na masa wani tunani daban bayan yaji tarihinsu. Zuciyarsa na cigaba da tunzurashi akan yayi amfani da damar k'arshe wajen bincikensa, tunda yabi dukkanin sauran bai samu wani bakin zareba. To amma kuma wannan ai ba tarbiyyar Malam bahaushe baceba, daga baya kuma idan komai yafitofa? wane kallo kuma za'a masa?, shinma zata iya fahimtarsa kuwa? dan irin wannan abun yakan farune a labaran films ko Novels, to amma wannan ce damarsa ta k'arshe ai kawai, dolene ya jefi tsuntsu biyu da dutsi d'aya kenan?.............✍🏼 Tirk'ashi, Nikam dai nakasa fahimtar wannan cirkud'ad'd'en tunanin na Galadima☹, fan's koku kun fahimta Ku fassara mana🤔?. *_Ya ALLAH ka gafartama iyayenmu😭👏🏻_* Qanwata don Allah ki karo min irin wa'innan hotunan,Tare kuma da na twins maza daban mata daban amman manya da kuma wanda duk suke a hade *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣5⃣ .......Tunda yafara tafiya bai tsaya ko inaba sai a wata sabuwar anguwa, shiru anguwar take babu yawan hayaniya, dan gidajenma tsilli-tsilli suke tamkar rugar Fulani, wani gida dakecan nesa da sauran gidajen yanufa, gidane babba mai k'aton bak'in gate, yay horn sau biyu akazo aka bud'e masa. a babbar harabar gidan yay parking, yana cikin motar bai fitoba har kusan 10 minutes bayan yagama waya yace ya iso. Idanu na zaro waje saboda ganin Muftahu yafito daga wata k'ofa yanufo motar, gaba d'aya mamaki yahanani kwakwkwaran motsi harya k'araso. Mai taxi yafito ya risina ya gaidashi, sannan yace nagama aikina Oga. Murmushi Muftahu yayi, sannan ya lek'a Munaya dake barci kashir6an ta glass, janye kansa yayi sannan ya zaro wayarsa daga aljihu yay kiran wani. “Umh yalla6ai akwai 'Yar matsala fa, dan barci takeyi sosai, kona d'akkota”. Da sauri yace “No ina zuwa, amma wannan driver dayay aikin yabar wajen, dan bana buk'atar ya ganni”. Murmuahi Muftahu yayi, tare da fad'in “angama ranka ya dad'e”. Muftahu ya sallami drivern daya kawo Munaya, yace zai kirashi ya maidata zuwa anjima, yaje yabar motar anan. “babu damuwa Oga, saina jika”. Bayan tafiyar driver Galadima yafito, dama duk yana kallon abinda ke faruwa ta window. Taku yake cikin tsantsar nuna jinin mulki dake yawo ajikinsa, ga wata izza ta zamowarsa cikakken namiji mai isashshiyar lafiya. fusakarnan babu walwala kamar kullum, ahaka ya k'araso wajen motar, Muftahu ya bud'e masa murfin inda Munaya ke kwance tana kwasar barcinta. Kallonta yayi na tsayin mintuna uku, sannan ya janye idonsa ya rankwafo da kansa cikin motar, saida yad'an cije lips d'insa sannan yasaka hannayensa biyu ya tallafota ahankali ya fito da ita, tamkar 'Yar baby haka ya d'akkota acikin hannayensa, sai wani kuma d'aure fuska yakeyi yana kauda kai, kaikace anmasa dolene ya d'auketa. Hannu Muftahu yasaka yatoshe bakinsa saboda dariyar dake Neman kwace masa. Wai yau Galadima gudane d'auke da mace a hannu, mutumin da ko kallon mata bai cika yiba, inkaga yana walwala ko dariya wa mace to Momma ce ko aunty Mimi. Jakarta ya d'auka shima yabi bayansa. Ya iske harya shinfid'eta a doguwar kujerar dake falon, yana gyara hannun rigarsa daya nannad'e yana jan k'aramin tsaki, ganin Muftahu na murmushi saiya kuma had'e fuska, Muftahu ya ajiye bag d'in yana had'iye dariyar da k'yar saboda gudun yin laifi. Hannu yamik'ama Muftahu. Muftahu yabashi handkerchief d'in daya zaro a aljihu, rankwafowa yayi kanta ya d'ora Handkerchief d'in bisa hancinta, tsayin minti 2 ya janye. Tari tafarayi, saikuma ta fara k'ok'arin bud'e idanunta tana lumshewa, Muftahu ya mik'o masa gorar ruwa mai d'an sanyi. Cikin hannunsa ya tsiyaya kad'an ya shafa mata a fuska, ahankali ta fara bud'e idanun ta, shikuma yaja da baya yakoma ya zauna bisa kujerar mai zaman mutum d'aya. d'ora k'afa yayi d'aya kan d'aya ya jingina kansa jikin kujerar ya lumshe idanu, saika rantse idonsa arufe suke, amma ya zubasune akan Munaya dake ta mutsu-mutsun tashi zaune. Da k'yar ta iya tashi ta samu ta jingina da kujerar tana k'arema falon kallo, yayinda hawaye ke zirara a kumatunta. Ruwa Muftahu ya mik'a mata, babu musu ta kar6a dan wata kishirwa takeji, tunda tafara shan ruwan bata ajiyeba saida ta shanye tas, nan wata zufa tafara karyo mata kuma. Mik'ewa Muftahu yayi yak'ara gudun AC n. Ahankali zufar tafara tsanewa, saikuma tad'anji k'arfin jikinta, Muryarta na rawa alamun kuka tace, “Please Ku suwaye? miyasa kuka kawoni nan? dan ALLAH kuyi hak'uri karku cutar dani, karku lalatamin rayuwa dan girman ALLAH, Ku tausayama mahaifiyata, damuwar damuke ciki kad'ai ta ishemu, wlhy daku keta mutuncina gwamma Ku kasheni yafimin sauk'i”. Daga Muftahu har uban gayyar kallonta kawai sukeyi, ita ko kad'anma bata gane Galadima ba, saboda yayi sama da fuskarsa. Muftahu ne yace “ki kwantar da hankalinki, kuma ba abinda yasa muka d'akkokiba kenan”. “to miyasa kuka d'akkoni? bawan ALLAH, mina muku?”. Muftahu ya juya ya kalli Galadima, amma saiyaga ko motsawa baiyiba, bashima da niyyar tanka musu. Itama Munaya saita maida kallon nata ga Galadima, a kuma lokacinne yad'ago kansa zai gyara zama. Wata razananniyar k'ara Munaya tasaki saboda tsorata, da Sauri Galadima ya toshe kunnensa, shima tsawar ya Daka mata wadda tasakata nutsuwar dole. “k!!! Dalla karki ciremana dodon kunni!!!!”. Dole Munaya tayi shiru jikinta na 6ari da k'yarma. Yaja wani wawan tsaki, tare da janye hannayensa daga kunnensa yana harara Munaya. “k wace irin shashashace ne?”. Sukda halin da take ciki saida ta watsa masa harara, amma bata iya cewa komaiba. Hannu yakai tamkar zai maketa saikuma ya FASA, komi yatuna oho. Komawa yayi inda yataso ya zauna, ya maida k'afafunsa yay crossing d'insu. Shi dai Muftahu yana kallonsu yakasa cewa komai, bakajin motsin komai saina shashshekar kukan Munaya Dana k'arar AC. Cikin kuka tace “minamaka kasa aka kawoni nanan? ko sokake kakuma jamin wani sabon 6atancin bayan Wanda yafaru abaya? wane Abu na tare maka waishin aduniyarnan dan ALLAH bawan ALLAH?”. takuma rushewa da kuka mai tsuma rai. Bakinsa ya ta6e a zuciyarsa yake fad'in daganin yarinyarnan akwai tsiwa dai, saikuma uban tsoro kamar farar kura. banza yamata, azahiri idonsa a lumshe suke, amma kuma abad'ini yana kallon Munaya ne, kukanta Neman saka masa ciwon kai yakeyi, dan haka yay maganar cikeda izza da mulki. “kinutsu muyi abinda ya kawomu, inba hakaba zaki kwana anan gidan ne”. Da Sauri Munaya ta share hawayenta, “indai kukane na daina wlhy, kayi hak'uri ka sanarmin, dan ALLAH ka maidani gida kafin hankalin innarmu ya tashi”. tak'are maganar da share hawaye. Dariya taso bashi amma saiya gimtse, saikace ba itace tagama tsiwa ba yanzun. Muftahu dai kasa hak'uri yayi saida yad'an dara, Galadima ya balla masa harara, hakanne yasashi yin shiru ya had'iye dariyar. “kin shirya tafiya kenan?”. ‘galadima yafad'a tamkar an masa dole sai yayi maganar’. Munaya tace, “wlhy na shirya ranka ya dad'e”. Yace “good girl” yana ta6e baki. “ki fad'amin waye yasaki aikin nan?”. Cikeda rashin fahimta Munaya tace, “wane aikin?”. Shiru Galadima yayi bai tanka ba, sai Muftahu ne yaymata bayani dalla-dalla akan abinda yafaru a plaza kwanakin baya”. Cikeda k'unar zuciya Munaya tace “ni babu Wanda yasakani, saima tozarci da hakan ya jawo mana muda mahaifiyarmu, bansan komaiba, amma tunda al amarinan yafaru muka kuma tsintar kanmu a k'unci, kullum da irin abin kuka dazamu gani agidanmu, yanzu haka akan waccan abin maganar aurena sau biyu tana lalacewa, yanzu haka satina guda kenan da baro asibiti saboda tashin hankalin dana shiga a dalilin fasa aurena da cin zarafi dana fuskanta daga Wanda yafasa aurena nawa, wlhy Ku yarda dani bansan komaiba”. Muftahu ya juya yana kallon Galadima da idonsa ke a rufe, amma yana sauraren Munayar. Kusan mintuna 3 sannan ya bud'e idonsa, akan Munaya ya zubasu, bazata iya jurar kallon kwayar idonsa ba dan haka tayi azamar janye nata, shima janye nasa yayi ya gyara zamansa. “kince babu hannunki? amma miya kaiki plaza a wannan time d'in daya kamata duk yarinyar kwarai tana gidansu?”. “Muna bikine, bayan munkai amare mun dawo sai fu'aad yamatsa akan saimun shiga, ba dan nasoba nayarda, kuma bani kad'ai baceba, harda 'yan uwana su uku”. “waye shi Fu'aad d'in?”. “Saurayinane, awajen bikin muka had'u dashi”. da sauri Galadima yace “miye kamaninsa? kuma ya kukayi dashi bayan abin ya faru?”. A nutse Munaya tabasu labarin komai, sannan ta zano musu kamannin Fu'aad dalla-dalla, danma bawani kallon tsaf tamasa ba a cikin kwana biyun. Muftahu yace “kozamu iya samun Horton shi Fu'aad d'in?”. “banida hotonsa, dan bai yarda munyi ko photo d'aya ba awajen bikin, amma zamu iya samu a video d'in da akayi maybe awajen dinner? ”. “galadima yace “a ina zamu CD d'in yanzu?”. “gaskiya wannan shine mai wahala, dan bansan taka maimai cikin angunan waye yasaka ayiba”. Galadima ya cije lips d'insa da k'arfi, sai kace zai hudasune. Kusan mintuna 3 kowa baice komaiba, sai can munaya tace “kunji na fad'a muku gaskiya, Ku maidani kafin afara nemana”. “zamu maidaki bisa sharad'i guda d'aya”. ‘cewar Muftahu ’. “wane sharad'ine?”. ‘Munaya ta tambaya’. “Sharad'in shine zakuyi auren 1year keda Galadima”. Cikin zaro idanu waje munaya tace “kamar ya? ban fahim cekaba fa?”. “ina nufin Auren yarjejeniya zakuyi na shekara 1 ko 2, ta wannan hanyarne kawai zamu iya kamo bakin zaren, sannan kekuma zaki sama ma iyayenki kwanciyar hankali, nanda kafin adadin da aka d'ibama auren yacika kinga komai ya wuce, saiya sakeki kiyi idda ki sami Wanda kikeso sannan kuje gida a d'aura miki aure dashi, Galadima ma zai iya sawa har auren a d'aura muku, daga baya sai kuje ya warwarema iyayenki komai, yakika gani?”. “tabd'i, wannan wace irin maganace saikace labarin Novels ko films? to tayayama za'ayi hakan yafaru? bayan nama sanarma iyayena banida wata alak'a dashi”. Murmuahi Muftahu yayi, yace “dan wannan duk mai sauk'ine, kedai amincewarki kawai muke nema”. “amma dai kun maidani wawuya wlhy, to ban aminceba, gara na dawwama banyi aureba ai”. Baki Muftahu ya bud'e zai k'ara magana Galadima ya d'aga masa hannu alamar yayi shiru ya barta. “kinga tashi kije kawai, amma wannan maganar tazama iyamu ukunnan, idan najita awani waje saina zubar miki da hanjin ciki waje, duk shawarar dakika Yanke da zuciyarki zaki iya nemanmu daga nan zuwa kwana biyu kawai”. Da sauri Munaya tazaro idanu waje tana kallon Galadima. Harara ya zuba mata yace “karki cinyeni”. Baki ta zun6ura gaba tana k'unk'uni, bayajin mitake fad'a, sai motsin la66anta kawai yake gani. Sai da aka rufemin iso sannan aka baro gidan dani, bankuma kwanceba saida motar ta tsaya, Wanda yake tare dani yacire k'yallen sannan yace na fita. Ko kallonsa banyiba saboda tsoro nafice amotar da sassarfa. Gudu-gudu sauri-sauri na Isa gidanmu, mutane sai kallona sukeyi, ALLAH ma yasoni babu kowa a tsakar gida, inaga matan gidan duk sun shige sallar magriba yaran kuma basu dawo daga islamiyya ba. A 6angarenmu ma innarmu na d'akinta, hakanne yabani damar shigewa d'akinmu wuff, na iske Munubiya na barci itama, na sauke ajiyar zuciya mai k'arfi ganin ALLAH ya tsareni babu Wanda ya ganni, kayana nacire daketa kamshin turaren Galadima, bayi nashige nida kayan, nayi wanka sannan suma na wankesu na shanya a bathroom d'in. Harna fito Munubiya bata tashiba, nayi sallar magriba sannan nafito wajen innarmu. Da mamaki take kallona, “yoni har ina shirin kiranki naji lfy baki dawoba had dare yarufa?”. Zama nayi ina murmushin yak'e, dan abinda yafaru tsakanina dasu Galadima d'anzu ya min kane-kane a zuciya. ganin abin nakeyi kamar a mafarki. “ayya innarmu ai tun d'azun nashigo, lokacin kina salla, harfa nayi wanka ma nad'an huta. tace tana gidaki, yaya jikin Munubiya?”. Jikinta Alhmdllh, tad'an watsa ruwa takoma ta kwanta bayan taci d'an abinci”. To Almdllh, ALLAH yak'ara afuwa. Amin innarmu ta amsamin, daganan muka koma hirar gidan Inna lami. Munkai tsawon lokaci afalon muna hira da innarmu, sai dai nifa bama fahimtar hirar nakeba, dan fili kawai nakeson samu nayin tunanin maganar su galadima. ★★★★ Tun bayan tafiyar Munaya Galadima yakoma kan doguwar kujerar yay kwanciyarsa tamkar mai barci. Muftahu dake kallonsa yace, “Amma miyasa kace ta tafi? batareda ta bamu gamsashshiyar amsa ba kuma?”. Shiru Galadima bai amsaba tsawon mintuna uku, sai zuwa can yabud'e idonsa yana kallon Muftahu, baki yad'an ta6e “karka damu kanka, tama yarda, amsa ce kawai bata bamuba, itama kuma zata bayarne, tuni naga yardarta cikin kwayar idonta, akwai abinda take shakku akansa shiyyasa tak'i amsa mana”. Kai Muftahu ya jinjina kawai, yasan tunda Galadima yafad'i haka to hakanne kuwa, amma sai yace “to amma bamu bata koda number ba, tayaya zata sanar damu amincewar tata kenan?”. Murmushi kawai Galadima yayi baice komaiba. Hakanne ya tabbatarma Muftahu murmushin Galadima shine amsar tambayarsa. Daga nan bai sake cemasa komaiba shima. Falon yay tsit. ★★★★ Gaba d'aya a kwanaki biyunan banida wani sukuni, tunanin maganar yak'i barin zuciyata, a kowacce dak'ik'a zuciyata tunzurani takeyi akan Na amince kawai, dan banida wata mafita sai wannan, ni kaina inason sanin Wanda ya aikata mana wannan abun, sannan bana fata sauran 'yan uwana suyi aure su barni a gidannan, hakan ba k'aramin tozarci zai zamarminba, ga Munubiya tadage akan innarmu ta sanarma Abba itama ad'aga bikinta har saina samu miji nima ahad'a ni da ita, na nuna mata 6acin raina akan maganar amma abanza, tanuna Sam ita tana a kan bakanta, nikuma harga ALLAH ba zanso hakan ta kasanceba. Ita kanta innarmu nakula danne zuciyata kawai takeyi akan fasa aurena, amma tana cikin matsananciyar damuwa. Yanzu yazanyi kenan? Na amince ko karna amince? gashi ya gargad'eni akan kadda Na nemi shawarar kowa, ni kaina nama kasa sanarma koda Munubiya, kuma kullum cikin tanbayata take mike damuna? duk da ita zatonta akan maganar Haidar ne har yanzu nake cikin damuwar. Yau dai kwanaki biyu kenan da faruwar abin, har yanzu kuma nakasa tsayawa a matsaya d'aya. Kusan tashin hantsi muna tsakar gida a baranda muduka 'yan matan gidan, kowa da hidimar dayakeyi, sai wasu daga cikin k'annenmu dake wasa agefenmu, iyayenmu kuma Na daga can k'arshen barandar suma kowa da hidimarta, innarmu ce kawai babu tana gidan mama Rabi'a taje duba feena da jikinta yad'an motsa. Tsayuwar mota mukaji a k'ofar gida, yara suka tafi da gudu dansuga wanene? azatonsu cikin su Dady ne. Mintuna baifi 10 ba saigasu suna shigowa da ledoji, saikuma ga Zarah tashigo cikin kwalliyar kece raini, tana taku d'ai-d'ai, daka ganta kaga mai yaron ciki, cikeda muran muka hau mata sannu dazuwa, itako saiwani ciccijewa take tana kuma Jan kai, ita adole matar manya. Abin kallo bai k'areba saida mamansu yaa Hameed ta iso da d'an gudu ta rungume Zarah a jikinta, duk mukai galala muna kallon wannan sabon salo. “masha ALLAHU Zarah sarkin haske, kinganki kuwa, da anganki anga matar manya yarinyata, kai ai aure Ni'ima ce babba, duk wacce ALLAH yabama 'yarta miji matan gidannan ta godema ALLAH, Dan wlhy yana sonta”. Caraf Momy Hadiza ta kar6e da fad'in “wlhy kuwa Yaya, ai babu babban bak'inciki irin kanada gandamemiyar budurwa a d'aki tayi kwantai takasa auruwa, aimu sai godiyar ubangiji wlhy, babu ta inda ni'ima bata saukar manaba, Zarah zoki zauna ki huta kinji 'yar albarka”. Maman safara'u da gwaggon haleema da maman su Fiddausi suka kwashe da dariya. Kowa yasan damu ake wannan gugar zanar, amma sai mukayi murmushi kawai bamuce komaiba, maman fauziyya ma batace komaiba, nama godema ALLAH da innarmu bata nan balle ranta ya 6aci. Tsam namik'e nabar wajen zuciyata Na suya, Na danne kukan dake shirin tahomin... Maman Safara'u tace, “to yanzu ke bazaki iya danne zuciyarki ba saikin nuna hasaadarki a filin ALLAH?, to Ashe ranar auren 'yan uwanki mutuwa kuwa zakiyi?, dan kina gani za'a d'auke kowacce abarki agidan. Wani k'arfine yazomin a zuciyata, Na had'iye kukana, najuyo ina kallonta ido cikin ido, wani murmushin takaici nasaki, sannan nace “maman Safara'u ke uwace agareni, sannan innarmu takoya mana tarbiyyar girmama kowacce mace agidannan, badan hakaba dana fad'a miki maganar dabazaki ta6a mantawaba, kuma ba hassadar tasani tashiba kamar yanda tunaninki yabaki, natashine Na d'aukama Zarah ruwansha, naga tashawo rana kuma babu Wanda yayi yink'urin bata”. Ina gama fad'ar haka nabar wajen. tsit banji kowa yasake maganar ba, bansan miyasa ba, maganar tawace tasakasu yin shiru kokuwa oho. Ina shiga falonmu Na fashe da kuka, anzo ga6ar da kawai zan amince da buk'atar Galadima, insha ALLAHU aranar datake fad'ar za'a tafi abarni, aranar nima zanbar gidan, Na gwammace nayi auren shekara d'ayan nafito. Tunanin tawace hanya zanbi Na fad'ar musu Na amince na farayi, dan basu bani number ko wata hanyaba dazan iya nemansu, gashi kuma bazan iya gane gidan dasuka kainiba. Tunawa dawata farar takarda nayi, wadda nagani a bag d'in dana fita da ita a ranar, kuma nasan ni bani Na ajiyeba. Da Sauri Na d'auki bag d'in na zazage, saiga takardar tafad'o, na d'auka na bud'e, Number wayace ajiki kawai. Jikina har rawa takeyi na d'auki wayata na kwafe number, sai kuma nakasa kira, na fara zagaye d'akin. Motsi naji kamar na tafiya, da Sauri na shige bathroom d'inmu dan nasan Munubiya ce. fanfo na kunna yanda zata d'auka wanka nakeyi. Sha warar tura massage kawai na yanke. dan haka na rubuta *_“na amince inhar bazai zama ka wulak'anta rayuwa taba”._* Haka kawai natura masa na cire kayana nafara wankan gaskiya...........✍🏼 ⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀time d'in wasa yafara.🤸🏻‍♀ *_Ya ALLAH ka gafartama iyayenmu_*👏🏻😭*_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣5⃣ .......Tunda yafara tafiya bai tsaya ko inaba sai a wata sabuwar anguwa, shiru anguwar take babu yawan hayaniya, dan gidajenma tsilli-tsilli suke tamkar rugar Fulani, wani gida dakecan nesa da sauran gidajen yanufa, gidane babba mai k'aton bak'in gate, yay horn sau biyu akazo aka bud'e masa. a babbar harabar gidan yay parking, yana cikin motar bai fitoba har kusan 10 minutes bayan yagama waya yace ya iso. Idanu na zaro waje saboda ganin Muftahu yafito daga wata k'ofa yanufo motar, gaba d'aya mamaki yahanani kwakwkwaran motsi harya k'araso. Mai taxi yafito ya risina ya gaidashi, sannan yace nagama aikina Oga. Murmushi Muftahu yayi, sannan ya lek'a Munaya dake barci kashir6an ta glass, janye kansa yayi sannan ya zaro wayarsa daga aljihu yay kiran wani. “Umh yalla6ai akwai 'Yar matsala fa, dan barci takeyi sosai, kona d'akkota”. Da sauri yace “No ina zuwa, amma wannan driver dayay aikin yabar wajen, dan bana buk'atar ya ganni”. Murmuahi Muftahu yayi, tare da fad'in “angama ranka ya dad'e”. Muftahu ya sallami drivern daya kawo Munaya, yace zai kirashi ya maidata zuwa anjima, yaje yabar motar anan. “babu damuwa Oga, saina jika”. Bayan tafiyar driver Galadima yafito, dama duk yana kallon abinda ke faruwa ta window. Taku yake cikin tsantsar nuna jinin mulki dake yawo ajikinsa, ga wata izza ta zamowarsa cikakken namiji mai isashshiyar lafiya. fusakarnan babu walwala kamar kullum, ahaka ya k'araso wajen motar, Muftahu ya bud'e masa murfin inda Munaya ke kwance tana kwasar barcinta. Kallonta yayi na tsayin mintuna uku, sannan ya janye idonsa ya rankwafo da kansa cikin motar, saida yad'an cije lips d'insa sannan yasaka hannayensa biyu ya tallafota ahankali ya fito da ita, tamkar 'Yar baby haka ya d'akkota acikin hannayensa, sai wani kuma d'aure fuska yakeyi yana kauda kai, kaikace anmasa dolene ya d'auketa. Hannu Muftahu yasaka yatoshe bakinsa saboda dariyar dake Neman kwace masa. Wai yau Galadima gudane d'auke da mace a hannu, mutumin da ko kallon mata bai cika yiba, inkaga yana walwala ko dariya wa mace to Momma ce ko aunty Mimi. Jakarta ya d'auka shima yabi bayansa. Ya iske harya shinfid'eta a doguwar kujerar dake falon, yana gyara hannun rigarsa daya nannad'e yana jan k'aramin tsaki, ganin Muftahu na murmushi saiya kuma had'e fuska, Muftahu ya ajiye bag d'in yana had'iye dariyar da k'yar saboda gudun yin laifi. Hannu yamik'ama Muftahu. Muftahu yabashi handkerchief d'in daya zaro a aljihu, rankwafowa yayi kanta ya d'ora Handkerchief d'in bisa hancinta, tsayin minti 2 ya janye. Tari tafarayi, saikuma ta fara k'ok'arin bud'e idanunta tana lumshewa, Muftahu ya mik'o masa gorar ruwa mai d'an sanyi. Cikin hannunsa ya tsiyaya kad'an ya shafa mata a fuska, ahankali ta fara bud'e idanun ta, shikuma yaja da baya yakoma ya zauna bisa kujerar mai zaman mutum d'aya. d'ora k'afa yayi d'aya kan d'aya ya jingina kansa jikin kujerar ya lumshe idanu, saika rantse idonsa arufe suke, amma ya zubasune akan Munaya dake ta mutsu-mutsun tashi zaune. Da k'yar ta iya tashi ta samu ta jingina da kujerar tana k'arema falon kallo, yayinda hawaye ke zirara a kumatunta. Ruwa Muftahu ya mik'a mata, babu musu ta kar6a dan wata kishirwa takeji, tunda tafara shan ruwan bata ajiyeba saida ta shanye tas, nan wata zufa tafara karyo mata kuma. Mik'ewa Muftahu yayi yak'ara gudun AC n. Ahankali zufar tafara tsanewa, saikuma tad'anji k'arfin jikinta, Muryarta na rawa alamun kuka tace, “Please Ku suwaye? miyasa kuka kawoni nan? dan ALLAH kuyi hak'uri karku cutar dani, karku lalatamin rayuwa dan girman ALLAH, Ku tausayama mahaifiyata, damuwar damuke ciki kad'ai ta ishemu, wlhy daku keta mutuncina gwamma Ku kasheni yafimin sauk'i”. Daga Muftahu har uban gayyar kallonta kawai sukeyi, ita ko kad'anma bata gane Galadima ba, saboda yayi sama da fuskarsa. Muftahu ne yace “ki kwantar da hankalinki, kuma ba abinda yasa muka d'akkokiba kenan”. “to miyasa kuka d'akkoni? bawan ALLAH, mina muku?”. Muftahu ya juya ya kalli Galadima, amma saiyaga ko motsawa baiyiba, bashima da niyyar tanka musu. Itama Munaya saita maida kallon nata ga Galadima, a kuma lokacinne yad'ago kansa zai gyara zama. Wata razananniyar k'ara Munaya tasaki saboda tsorata, da Sauri Galadima ya toshe kunnensa, shima tsawar ya Daka mata wadda tasakata nutsuwar dole. “k!!! Dalla karki ciremana dodon kunni!!!!”. Dole Munaya tayi shiru jikinta na 6ari da k'yarma. Yaja wani wawan tsaki, tare da janye hannayensa daga kunnensa yana harara Munaya. “k wace irin shashashace ne?”. Sukda halin da take ciki saida ta watsa masa harara, amma bata iya cewa komaiba. Hannu yakai tamkar zai maketa saikuma ya FASA, komi yatuna oho. Komawa yayi inda yataso ya zauna, ya maida k'afafunsa yay crossing d'insu. Shi dai Muftahu yana kallonsu yakasa cewa komai, bakajin motsin komai saina shashshekar kukan Munaya Dana k'arar AC. Cikin kuka tace “minamaka kasa aka kawoni nanan? ko sokake kakuma jamin wani sabon 6atancin bayan Wanda yafaru abaya? wane Abu na tare maka waishin aduniyarnan dan ALLAH bawan ALLAH?”. takuma rushewa da kuka mai tsuma rai. Bakinsa ya ta6e a zuciyarsa yake fad'in daganin yarinyarnan akwai tsiwa dai, saikuma uban tsoro kamar farar kura. banza yamata, azahiri idonsa a lumshe suke, amma kuma abad'ini yana kallon Munaya ne, kukanta Neman saka masa ciwon kai yakeyi, dan haka yay maganar cikeda izza da mulki. “kinutsu muyi abinda ya kawomu, inba hakaba zaki kwana anan gidan ne”. Da Sauri Munaya ta share hawayenta, “indai kukane na daina wlhy, kayi hak'uri ka sanarmin, dan ALLAH ka maidani gida kafin hankalin innarmu ya tashi”. tak'are maganar da share hawaye. Dariya taso bashi amma saiya gimtse, saikace ba itace tagama tsiwa ba yanzun. Muftahu dai kasa hak'uri yayi saida yad'an dara, Galadima ya balla masa harara, hakanne yasashi yin shiru ya had'iye dariyar. “kin shirya tafiya kenan?”. ‘galadima yafad'a tamkar an masa dole sai yayi maganar’. Munaya tace, “wlhy na shirya ranka ya dad'e”. Yace “good girl” yana ta6e baki. “ki fad'amin waye yasaki aikin nan?”. Cikeda rashin fahimta Munaya tace, “wane aikin?”. Shiru Galadima yayi bai tanka ba, sai Muftahu ne yaymata bayani dalla-dalla akan abinda yafaru a plaza kwanakin baya”. Cikeda k'unar zuciya Munaya tace “ni babu Wanda yasakani, saima tozarci da hakan ya jawo mana muda mahaifiyarmu, bansan komaiba, amma tunda al amarinan yafaru muka kuma tsintar kanmu a k'unci, kullum da irin abin kuka dazamu gani agidanmu, yanzu haka akan waccan abin maganar aurena sau biyu tana lalacewa, yanzu haka satina guda kenan da baro asibiti saboda tashin hankalin dana shiga a dalilin fasa aurena da cin zarafi dana fuskanta daga Wanda yafasa aurena nawa, wlhy Ku yarda dani bansan komaiba”. Muftahu ya juya yana kallon Galadima da idonsa ke a rufe, amma yana sauraren Munayar. Kusan mintuna 3 sannan ya bud'e idonsa, akan Munaya ya zubasu, bazata iya jurar kallon kwayar idonsa ba dan haka tayi azamar janye nata, shima janye nasa yayi ya gyara zamansa. “kince babu hannunki? amma miya kaiki plaza a wannan time d'in daya kamata duk yarinyar kwarai tana gidansu?”. “Muna bikine, bayan munkai amare mun dawo sai fu'aad yamatsa akan saimun shiga, ba dan nasoba nayarda, kuma bani kad'ai baceba, harda 'yan uwana su uku”. “waye shi Fu'aad d'in?”. “Saurayinane, awajen bikin muka had'u dashi”. da sauri Galadima yace “miye kamaninsa? kuma ya kukayi dashi bayan abin ya faru?”. A nutse Munaya tabasu labarin komai, sannan ta zano musu kamannin Fu'aad dalla-dalla, danma bawani kallon tsaf tamasa ba a cikin kwana biyun. Muftahu yace “kozamu iya samun Horton shi Fu'aad d'in?”. “banida hotonsa, dan bai yarda munyi ko photo d'aya ba awajen bikin, amma zamu iya samu a video d'in da akayi maybe awajen dinner? ”. “galadima yace “a ina zamu CD d'in yanzu?”. “gaskiya wannan shine mai wahala, dan bansan taka maimai cikin angunan waye yasaka ayiba”. Galadima ya cije lips d'insa da k'arfi, sai kace zai hudasune. Kusan mintuna 3 kowa baice komaiba, sai can munaya tace “kunji na fad'a muku gaskiya, Ku maidani kafin afara nemana”. “zamu maidaki bisa sharad'i guda d'aya”. ‘cewar Muftahu ’. “wane sharad'ine?”. ‘Munaya ta tambaya’. “Sharad'in shine zakuyi auren 1year keda Galadima”. Cikin zaro idanu waje munaya tace “kamar ya? ban fahim cekaba fa?”. “ina nufin Auren yarjejeniya zakuyi na shekara 1 ko 2, ta wannan hanyarne kawai zamu iya kamo bakin zaren, sannan kekuma zaki sama ma iyayenki kwanciyar hankali, nanda kafin adadin da aka d'ibama auren yacika kinga komai ya wuce, saiya sakeki kiyi idda ki sami Wanda kikeso sannan kuje gida a d'aura miki aure dashi, Galadima ma zai iya sawa har auren a d'aura muku, daga baya sai kuje ya warwarema iyayenki komai, yakika gani?”. “tabd'i, wannan wace irin maganace saikace labarin Novels ko films? to tayayama za'ayi hakan yafaru? bayan nama sanarma iyayena banida wata alak'a dashi”. Murmuahi Muftahu yayi, yace “dan wannan duk mai sauk'ine, kedai amincewarki kawai muke nema”. “amma dai kun maidani wawuya wlhy, to ban aminceba, gara na dawwama banyi aureba ai”. Baki Muftahu ya bud'e zai k'ara magana Galadima ya d'aga masa hannu alamar yayi shiru ya barta. “kinga tashi kije kawai, amma wannan maganar tazama iyamu ukunnan, idan najita awani waje saina zubar miki da hanjin ciki waje, duk shawarar dakika Yanke da zuciyarki zaki iya nemanmu daga nan zuwa kwana biyu kawai”. Da sauri Munaya tazaro idanu waje tana kallon Galadima. Harara ya zuba mata yace “karki cinyeni”. Baki ta zun6ura gaba tana k'unk'uni, bayajin mitake fad'a, sai motsin la66anta kawai yake gani. Sai da aka rufemin iso sannan aka baro gidan dani, bankuma kwanceba saida motar ta tsaya, Wanda yake tare dani yacire k'yallen sannan yace na fita. Ko kallonsa banyiba saboda tsoro nafice amotar da sassarfa. Gudu-gudu sauri-sauri na Isa gidanmu, mutane sai kallona sukeyi, ALLAH ma yasoni babu kowa a tsakar gida, inaga matan gidan duk sun shige sallar magriba yaran kuma basu dawo daga islamiyya ba. A 6angarenmu ma innarmu na d'akinta, hakanne yabani damar shigewa d'akinmu wuff, na iske Munubiya na barci itama, na sauke ajiyar zuciya mai k'arfi ganin ALLAH ya tsareni babu Wanda ya ganni, kayana nacire daketa kamshin turaren Galadima, bayi nashige nida kayan, nayi wanka sannan suma na wankesu na shanya a bathroom d'in. Harna fito Munubiya bata tashiba, nayi sallar magriba sannan nafito wajen innarmu. Da mamaki take kallona, “yoni har ina shirin kiranki naji lfy baki dawoba had dare yarufa?”. Zama nayi ina murmushin yak'e, dan abinda yafaru tsakanina dasu Galadima d'anzu ya min kane-kane a zuciya. ganin abin nakeyi kamar a mafarki. “ayya innarmu ai tun d'azun nashigo, lokacin kina salla, harfa nayi wanka ma nad'an huta. tace tana gidaki, yaya jikin Munubiya?”. Jikinta Alhmdllh, tad'an watsa ruwa takoma ta kwanta bayan taci d'an abinci”. To Almdllh, ALLAH yak'ara afuwa. Amin innarmu ta amsamin, daganan muka koma hirar gidan Inna lami. Munkai tsawon lokaci afalon muna hira da innarmu, sai dai nifa bama fahimtar hirar nakeba, dan fili kawai nakeson samu nayin tunanin maganar su galadima. ★★★★ Tun bayan tafiyar Munaya Galadima yakoma kan doguwar kujerar yay kwanciyarsa tamkar mai barci. Muftahu dake kallonsa yace, “Amma miyasa kace ta tafi? batareda ta bamu gamsashshiyar amsa ba kuma?”. Shiru Galadima bai amsaba tsawon mintuna uku, sai zuwa can yabud'e idonsa yana kallon Muftahu, baki yad'an ta6e “karka damu kanka, tama yarda, amsa ce kawai bata bamuba, itama kuma zata bayarne, tuni naga yardarta cikin kwayar idonta, akwai abinda take shakku akansa shiyyasa tak'i amsa mana”. Kai Muftahu ya jinjina kawai, yasan tunda Galadima yafad'i haka to hakanne kuwa, amma sai yace “to amma bamu bata koda number ba, tayaya zata sanar damu amincewar tata kenan?”. Murmushi kawai Galadima yayi baice komaiba. Hakanne ya tabbatarma Muftahu murmushin Galadima shine amsar tambayarsa. Daga nan bai sake cemasa komaiba shima. Falon yay tsit. ★★★★ Gaba d'aya a kwanaki biyunan banida wani sukuni, tunanin maganar yak'i barin zuciyata, a kowacce dak'ik'a zuciyata tunzurani takeyi akan Na amince kawai, dan banida wata mafita sai wannan, ni kaina inason sanin Wanda ya aikata mana wannan abun, sannan bana fata sauran 'yan uwana suyi aure su barni a gidannan, hakan ba k'aramin tozarci zai zamarminba, ga Munubiya tadage akan innarmu ta sanarma Abba itama ad'aga bikinta har saina samu miji nima ahad'a ni da ita, na nuna mata 6acin raina akan maganar amma abanza, tanuna Sam ita tana a kan bakanta, nikuma harga ALLAH ba zanso hakan ta kasanceba. Ita kanta innarmu nakula danne zuciyata kawai takeyi akan fasa aurena, amma tana cikin matsananciyar damuwa. Yanzu yazanyi kenan? Na amince ko karna amince? gashi ya gargad'eni akan kadda Na nemi shawarar kowa, ni kaina nama kasa sanarma koda Munubiya, kuma kullum cikin tanbayata take mike damuna? duk da ita zatonta akan maganar Haidar ne har yanzu nake cikin damuwar. Yau dai kwanaki biyu kenan da faruwar abin, har yanzu kuma nakasa tsayawa a matsaya d'aya. Kusan tashin hantsi muna tsakar gida a baranda muduka 'yan matan gidan, kowa da hidimar dayakeyi, sai wasu daga cikin k'annenmu dake wasa agefenmu, iyayenmu kuma Na daga can k'arshen barandar suma kowa da hidimarta, innarmu ce kawai babu tana gidan mama Rabi'a taje duba feena da jikinta yad'an motsa. Tsayuwar mota mukaji a k'ofar gida, yara suka tafi da gudu dansuga wanene? azatonsu cikin su Dady ne. Mintuna baifi 10 ba saigasu suna shigowa da ledoji, saikuma ga Zarah tashigo cikin kwalliyar kece raini, tana taku d'ai-d'ai, daka ganta kaga mai yaron ciki, cikeda muran muka hau mata sannu dazuwa, itako saiwani ciccijewa take tana kuma Jan kai, ita adole matar manya. Abin kallo bai k'areba saida mamansu yaa Hameed ta iso da d'an gudu ta rungume Zarah a jikinta, duk mukai galala muna kallon wannan sabon salo. “masha ALLAHU Zarah sarkin haske, kinganki kuwa, da anganki anga matar manya yarinyata, kai ai aure Ni'ima ce babba, duk wacce ALLAH yabama 'yarta miji matan gidannan ta godema ALLAH, Dan wlhy yana sonta”. Caraf Momy Hadiza ta kar6e da fad'in “wlhy kuwa Yaya, ai babu babban bak'inciki irin kanada gandamemiyar budurwa a d'aki tayi kwantai takasa auruwa, aimu sai godiyar ubangiji wlhy, babu ta inda ni'ima bata saukar manaba, Zarah zoki zauna ki huta kinji 'yar albarka”. Maman safara'u da gwaggon haleema da maman su Fiddausi suka kwashe da dariya. Kowa yasan damu ake wannan gugar zanar, amma sai mukayi murmushi kawai bamuce komaiba, maman fauziyya ma batace komaiba, nama godema ALLAH da innarmu bata nan balle ranta ya 6aci. Tsam namik'e nabar wajen zuciyata Na suya, Na danne kukan dake shirin tahomin... Maman Safara'u tace, “to yanzu ke bazaki iya danne zuciyarki ba saikin nuna hasaadarki a filin ALLAH?, to Ashe ranar auren 'yan uwanki mutuwa kuwa zakiyi?, dan kina gani za'a d'auke kowacce abarki agidan. Wani k'arfine yazomin a zuciyata, Na had'iye kukana, najuyo ina kallonta ido cikin ido, wani murmushin takaici nasaki, sannan nace “maman Safara'u ke uwace agareni, sannan innarmu takoya mana tarbiyyar girmama kowacce mace agidannan, badan hakaba dana fad'a miki maganar dabazaki ta6a mantawaba, kuma ba hassadar tasani tashiba kamar yanda tunaninki yabaki, natashine Na d'aukama Zarah ruwansha, naga tashawo rana kuma babu Wanda yayi yink'urin bata”. Ina gama fad'ar haka nabar wajen. tsit banji kowa yasake maganar ba, bansan miyasa ba, maganar tawace tasakasu yin shiru kokuwa oho. Ina shiga falonmu Na fashe da kuka, anzo ga6ar da kawai zan amince da buk'atar Galadima, insha ALLAHU aranar datake fad'ar za'a tafi abarni, aranar nima zanbar gidan, Na gwammace nayi auren shekara d'ayan nafito. Tunanin tawace hanya zanbi Na fad'ar musu Na amince na farayi, dan basu bani number ko wata hanyaba dazan iya nemansu, gashi kuma bazan iya gane gidan dasuka kainiba. Tunawa dawata farar takarda nayi, wadda nagani a bag d'in dana fita da ita a ranar, kuma nasan ni bani Na ajiyeba. Da Sauri Na d'auki bag d'in na zazage, saiga takardar tafad'o, na d'auka na bud'e, Number wayace ajiki kawai. Jikina har rawa takeyi na d'auki wayata na kwafe number, sai kuma nakasa kira, na fara zagaye d'akin. Motsi naji kamar na tafiya, da Sauri na shige bathroom d'inmu dan nasan Munubiya ce. fanfo na kunna yanda zata d'auka wanka nakeyi. Sha warar tura massage kawai na yanke. dan haka na rubuta *_“na amince inhar bazai zama ka wulak'anta rayuwa taba”._* Haka kawai natura masa na cire kayana nafara wankan gaskiya...........✍🏼 ⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀time d'in wasa yafara.🤸🏻‍♀ *_Ya ALLAH ka gafartama iyayenmu_*👏🏻😭 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣7⃣ .........Cikeda girmamawa yace, “Ranka ya dad'e barka da dare?”. “barkan ka dai Muhammad. dama kashigo k'asar kenan?”. Gabansa yad'an fad'i, danshifa yama manta mai martaba baisan yazo k'asarba, dakiyar dole ya aro yace, “wlhy kuwa nashigo d'azun yin wani aiki, amma gobema idan ALLAH ya kaimu zan koma”. “tofa, gobe gobe? kuma gashi inason ganinka a goben”. d'an jimm yayi, irin tamkar baisan komaiba, cikeda shakku yace, “ranka ya dad'e lafiya dai ko?”. “lafiya k'alau, wata muhimmiyar magana nakeson muyine”. “to shikenan, zanshigo insha ALLAH ”. “to madalla saina ganka”. Dafe kai Galadima yayi yana mamakin kansa, anya kuwa baima kansa d'aurin gorobo? koda yake idanfa yayi hak'uri shekara 1 ne ko 2 kacal, inma komai yafito kafin cikar shekarar zai sawwak'a matane, yad'an murmusa sannan yakoma ya kwanta abinsa cikeda tunani barkatai. ★★★★★ Rashin reply d'in Galadima ya dameni, haka dai naita danne zuciyata dankar innarmu da Munubiya su fahimta, nacigaba da harkokina tamkar banida wata damuwa a zuciya, saima sallar dare damuka fara dagewa da tashi nida Munubiya, gakuma azumin damuka tashi dashi yau litinin. Duk da innarmu ta fahimci inada damuwa batacemin uffanba, saidai tausayina na damun zuciyarta, tana dannewane kawai. Munubiya kam tsaf tagama fahimta ta, amma itama saita nuna bata fahimci komaiba, taje tasamu innarmu da maganar son a d'aga bikinta again. “munubiya ba wannan yakamata muyiba, addu'a yakamata muyima 'Yar uwarki, idan da rabo saikiga ALLAH ya kawo mata miji a cikin watanni 2nan dasuka rage kinji. nima nasan tana acikin damuwa, amma tana dannewa a zuciyarta saboda farin cikinmu. addu'ar dazamu mata itace tsantsar k'aunarta a garemu”. “shikenan innarmu, insha ALLAH zamu kuma dagewa da fad'ama ALLAH, itama ALLAH ya kawo mata ta hanyar da batayi zatoba, ya sakanka mata fiyeda sadaukarwar datayi, innarmu nasan sadaukarwar da 'Yar uwata tayine yasakata a wannan halin, ta sadaukar da farincikinta saboda ni, mizanyi na biyata nikam”. Murmushi innarmu tayi, tace, “addu'a”. ★★★★★ Washe gari yatashi ya shirin tafiya masarautar su Momma, Harun yakira yace ya nema masa ticket. Cikeda mamaki Harun yace, “yaushe kashigo k'asar Galadima?”. K'aramin tsaki yaja, dan shifa yama manta Harun baisan da zuwansa ba, Link d'in hannun rigar milk d'in shaddarsa yake k'okarin sakawa, cikeda dakiya yace, “jiya nazo da daddare, kuma inagama yau zan koma”. “tofa, amma baka cikin masarauta?”. “no a hotel Na sauka”. “ok barato a nema ticket d'in, sai muzo mu d'aukeka”. “karka damu harun, banason kowa yasan nazoma, muhad'u dakai kawai a airport ”. Koda suka yanke wayar sai yaja tsaki, gaba d'aya yakoma mak'aryaci, abinda yatsana arayuwarsa fiye da komai kenan (k'arya) amma sai gashi shi yana zundumata, “Astagafurullh” yashiga maimaitawa a zuciyarsa. Tsaf yafito cikin shadda milk color (nakula yana k'aunar milk) d'inkin rigar 3quarter, harda su hula, yayi k'yau sosai, yafito ainahin sa na cikakken bahaushe kuma basarake, ya fesa turaraensa Na kullum, komai nasa dayazo dashi ya had'a a waje d'aya. sannan yakashe kayan wutar bedroom d'in. Afalo ya iske Muftahu zaune yana jiransa, yad'anyi mamaki amma sai bai nunaba, yabashi hannu suka gaisa. Muftahu yace, “zaka dawo ta nan kenan?”.. Kai Galadima yad'aga alamar a'a, sannan yanufi kayan wutar falon yafara kashewa. saida yagama komai sannan ya kalli Muftahu alamar suje. Murmushi kawai Muftahu yayi, danya lura yau miskilawanne aka. Sun isa airport, lokacin shima harun harya je, mamakine ya kama harun Dan ganin Galadima tare da Muftahu, shima yanzu yana mamakin yanda Muftahu ke kuma kusanta kanshi da Galadima, baice komaiba yabashi hannu suka gaisa kamar yanda yabama Galadima. Harun yanason suyi magana da Galadima amma ga Muftahu a wajen, sai kawai yashare akan sayi a waya kawai. Basu wani dad'e a airport d'inba jirgin su Galadima yatashi. ★★★★ Yau hankalin kowa a tashe yake agidanmu saboda gwaggo Safiyya da aka kawo batada lafiya, dayake ba'anan kusa damu take aureba, tanacan wani gari daban, tun lokacin bikinsu yaa Hameed tamasu Abba complain akan batajin dad'i, amma kunsan maza darashin d'aukar Abu serious, sai basu maida hankalinsuba. Ita kuma kunya tahanata kuma musu maganar, har aka gama biki ta tafi, ashe baiwar ALLAH ciwo nata cin jikinta babu Wanda yasani, tun tanayi a tsitsaye har takai ga kwanciya, yaranta sun kaita asibiti amma basuga wani canjiba, hakanne yasa suka maidota gida, Dan aganinsu dai su Abba sunfi mahaifinsu k'arfi. Aiko suna isowa babu 6ata lokaci aka wuce da ita asibiti. Dan danan aka fara bata taimakon gaggawa. Muda innarmu ne kawai da innaro a asibitin, amma matan gidanmu babu wace tabimu, kusan mudasu baba k'arami muketa shiga da fita a asibitin dan ganin komai ya dai-daita. Kusan yamma saigasu Safara'u lokacin ma gwaggo Safiyya tana barci, yaranta duksunyi jigum-jigum da innaro saboda tashin hankalin dasuke ciki. Har dare ba'abar kowa yashiga wajen taba, sai su Dady kawai, ganin dare yayi akace mu muje gida kawai. Haka muka tafi akabar innaro da aunty habiba d'iyar gwaggo safiyyar ta uku, itama tayi aure amma tafito, yanzu zawarci takeyi. saikuma yaa Anas da aka barmusu saboda ko wani Abu zai taso. ★★★ Tunda yafito daga jirgi ya hango tawagar masarautar kakannin nasa, yasan tarbarsa sukazoyi, inhar zaishigo haka sukeyo gayyar tarbarsa, saikace wani bak'o daban, gefe yayi da fuskarsa dankarsu gansa, sashen motocin da akan d'auka drop ya nufa, duk manyan motocine da aka tanada dama domin irinsu, d'aya yabud'e da Kansa yashige da sauri, alamar yayma driver d'in suje. Tacikin glass yake kallonsu yana murmushi, yanda suketa d'aga kai nason hangosa, suna fita daga airport d'in ya kwantar da kansa ajikin seat ya lumshe idanunsa yana tunanin wane hukunci mai martaba zai yanke akan maganar, shin ya amincene? Kokuwa?. Driver yace, “oga ina muka nufa?”. Bai bud'e idonsaba kuma bai d'agoba, yace “gidan sarki”. Ta madubi driver n ya kallesa, “yalla6ai ko kaine ma dai akazo tarba daga masarauta?”. Murmushi kawai yayi batareda yace komaiba. Jin bai amsaba sai driver yakama bakinsa ya tauke shima. Ganin shine yasa dogarai suka bari aka shigar dashi har cikin masarauta, tunda yafito bayi da hadimai keta zubewa suna kwasar gaisuwa, hannu kawai yake d'aga musu, fuskarsa ad'an sake take, bai d'aureba baikumayi murmushi ko dariya ba kai tsaye. Tuni an kar6i kayansa an nufi sashin inno dasu, shikuma yanufi fada, Dan yasan yanzu Sarki suna fadanci. Cike fadar take da 'yan majalissar Sarki anata fadanci, bayan an masa iso yashiga da sallama, nanfa dogarai suka fara zuba masa kirari. Hannu kawai ya d'aga musu ya rissina yana mik'a gaisuwa ga Sarki. Sarki da fuskarsa tacika da fara'ar ganin jikan nasa ya amsa cikin lumshe idanu. Nan dogarai suka d'au da fad'in “sarki ya amsa maka sarkin gagara badau na gobe, an gaida magajin sarki, galadiman gagara badau, ALLAH yabaka zamani irinna sarki gagara badau. Galadima Yakuma rissinawa ya mik'a gaisuwa ga 'yan majissar sarki, suma cikeda fara'a suka amsa, kowa yasan irin tsantsar k'aunar da sarki kema jikan nasa a masarautar. Atake anan sarki ya sallami kowa, fadanci yatashi saikuma gobe idan ALLAH ya kaimu, yau yanada ganawa ta musamman da jikansa. Haka kowa yatashi yana musu addu'ar kasancewa cikin aminci. Tareda Galadima sarki yashiga cikin gidansa, hannunsa Na rik'e da Na Galadima, ba sabon Abu bane hakan a masarautar, duk Wanda yakwana yatashi acikinta yasan matsayin Galadima azukatan masu masarautar. Akatafaren falon sarki suka yada zango, babu dad'ewa da shigowarsu saiga jakadiya da kuyangi uku, kowanne d'aukeda babban tire, bayan sun dire komai suka zube suna kwasar gaisuwa wa sarki, sannan suka gaida Galadima. Jakadiya ma ta rissina ta gaida Galadima damasa barka da zuwa masarautarsu. Bayan fitarsu Galadima yakuma risainawa a girmame ya gaida sarki kakansa. Cike da murmushi sarki ya amsa yana kamo hannunsa, “Muhammad Sameer! kana lafiya”. “Alhmdllh ranka ya dad'e”. “Masha ALLAH, ya kabaromin Zeenah ta da jikin babanka da 'yan uwanka kuma su Haneefa?”. “Momma lafiyarta lau, hakama jikin Abie Alhmdllh, suma su aunty mimin haka”. “to Alhmdllhi, ALLAH yacigaba da jagorantar lamuranku ya albarkaci rayuwarku ta gobe da jibin jibima”. Murmushi Galadima yayi yana amsawa da amin. Sarki da Galadima tare sukaci abinci, (tun yana k'arami dama idan yazo gidan hakance ke faruwa tsakaninsu) Sunci sun k'oshi sukayi hamdala ga ALLAH. babu wani 6ata lokaci sarki yashiga masa bayanin kiran nasa akan maganar da Fateema (mom) tazo masa da itane jiya, shima ya zauna yayi nazari yagane hakan shine dai-dai, Galadima ya auri Munaya. tur6une fuska Galadima yayi tamkar baisan komaiba, yace “ranka yadad'e ka gafarceni, ammafa ni bata minba ai”. Sarki yay murmushinsu Na manyan k'asaitattun masu ji da mulki, “basai tayi makaba Muhammad, domin sanda Na aurama babanka Zeenah itama bai mataba, amma saboda biyayya dakuma tausayin d'iyar 'Yar uwarta ta amince tamin biyayya, to kaima hakan nakeso gareka, ka amsamin da to kawai saimu zauna lafiya, kasan magana biyu ba halina baceba ko”. Jinjina kai Galadima yayi yana kuma tankwashe k'afarsa, cikeda girmamawa yace “ALLAH ya huci zuciyarka ranka ya dad'e, Na amince da za6inka, ALLAH yabani ikon rik'ewa”. Cike da tsantsar farinciki Mai martaba ya rik'o hannun Galadima, “Muhammad ALLAH shiyi maka albarka, ya tsareka dadukkan sharri, ALLAH yabama mahaifinka lafiya kaji”. “amin ranka ya dad'e, ngd sosai ”. Daga nan hira suka cigaba dayi cikin tsantsar soyayya da k'aunar juna, kowanne yanajin d'an uwansa sosaih a ransa. Kusan atare suka yini, inno tun tana zuba idon shigowar Galadima harta hak'ura. Galadima bai shigo wajenta ba sai bayan sallar magriba. Tundaga k'ofar sashenta hadimai keta kwasar gaisuwa, tuni labarin tahowarsa ta iske inno, hakan yasa ta k'imtsa da k'yau, ta sallami bayinta masu mata hidima. Fuskarsa d'auke da k'ayataccen murmushi ya k'araso falon, bai zauna ko inaba sai jikin kakarsa, oh my sweet inno I miss you so much wlhy”. Kunnensa tad'anja kad'an, cikeda tsokana tace “miskili kafi mahaukaci ban haushi, aini harna fara shirin yo bikonka daga turakar mai martaba”. Yayi 'Yar dariya yana fad'in “tuba nake ginbiyar papi”. “ja'irin kaya, bazaka canjaba dai? ya kabaro iyayen naka da 'yan uwanka?”. “kowa lafiya lau ranki ya dad'e”. “to Alhmdllhi ”. Nanma hirarce ta 6alle tsakanin kaka da jikanta, kan mace me nanma an cika masa gaba da kayan itatuwa, shikuma yana zubama inno shagwa6ar daya saba tana biye masa. Masu jiran Galadima kuwa a airport saida sukaga kowa yagama fita ajirgi babushi sannan wani dogari yakira sarkin fada yake sanar dashi sufa basuga Galadima ba. Sarkin fada yace “yo kunacan kuna shashanci yaza'ayi Ku gansa, shi harma sun shige cikin gida da sarki ”. 'yan uwansa ya sanarmawa suka tattaro suka dawo masarautar.🤣 Dole a nan masarautar ya kwana, washe gari ya zagaya duka sashen sauran matan sarki ya gaidasu a mutunce. suma dai sunmasa tarbar mutunci kamar yanda suka saba, duk da dai taciki Na ciki. Sannan sai sassan iyayensa yayun momma da k'annenta, dukda dai bako ina yashigaba. Yanzunma tare sukayi karin kumallo da maimartaba, sannan suka fita fada tare, da Galadima akayi fadanci yau, yana gefen adalin kakansa. Washe gari da safe ya tattara inasa-inasa ya cane India, yabar tsofin da kewarsa, shima yatafi yana kewarsu. ******** Gwaggo Safiyya tacigaba da samun kulawa sosai, dukda dai tanad'an jin jiki, kullum matan gidanmu sukanzo sau d'aya, muma dai makaranta tasa bama yini a asibitin, amma kullum da safe mukanzo mu kuma dawo da yamma. Matan gidanmu kam jarabar innaro tasakasu k'ok'arin zuwa kullum, dan tace wlhy duk Wanda bata zuwa saitayi Dana sanin saninta. Wannan furuci ya d'an tsoratasu, dan kowa agidan yasan wacece innaro, idan kaga mutuncinku ya d'ore to kana cinna mata 'yan canji ta k'ark'ashin k'asane🙊, amma kana hanata gobe bazai hana ta karta maka rashin m ba🤣. (Ho innaro mu ta mutunci🤸🏻‍♀, ina yinki over ginbiyar Malam faruku😜🙊) ⛹🏻‍♀ Abin yafara tsoratani ganin har sati 1 dayin maganarmu dasu Galadima amma babuko labarinsu, tun ina saran yau gobe har na daina lissafin ma, ganin zan saka kaina a damuwa nacirema zancen a raina gaba d'aya, domin Na gama fahimtar maganar Galadima da abokinsa k'aryace, maybe ma mafarki nayi naketa shirmena kawai. A tsaitsaye damuwa tafara ramar dani a tsaye, sai idanuwa da dogon hanci. Tun ina daurewa har Abu yaso yaci tura, ciwon kai Dana k'irji suka fara zama abokaina. Ranar data kama sati biyu cif saiga bak'i su Abba sunyi, babu Wanda yasan daga ina suke, kuma su Abba basuma kowa bayanin komaiba dangane da bak'in. saida sukayi kwanaki uku da zuwa sannan naji wai wanine yakawo kud'in aurena yana son abama d'ansa. Lamarin yabama kowa mamaki, nanfa 'yan gidanmu suka hau dariyar mugunta wai kwantai dai ya tabbata kenan. Gugar zanar dasuke tayine ya fusata innarmu, tasakama Abba kuka akan bata aminceba, yaza'ayi su d'auki aurena subama mutumin dabasu saniba, idan su sun gaji dani itafa tanason kayarta. Lallashi duniya Abba yayi dan innarmu ta fahimta amma Sam tak'i saurararsa, wannan ne karon farko da yaga tsantsar fushinta. Yarasa yazai mata, dan shima lamarin Na damunsa, yarasa minene yasakashi amincewa yabada auren d'iyartasa ga mutanen?, shi dai kawai tsohon yamasa kwarjinine wlhy, dan jiyay ko kad'an bazai iya musa masaba. dukda talakawane kamarsa, harma yana ganin yafisu abubuwa da yawa. Lamarifa yayi tsamari a d'an tsakaninnan a gidanmu, dan innarmu takasa kwantar da hankalinta, hakama abbanmu, yayinda 'yan gidanmu sukejin Dad'i kamar su had'a fati. Nikuwa uwar gayya ai ba'a magana ma, nakira number Galadima yafi sau 200 amma tak'i shiga ko sau d'aya, lokaci guda nagama fita hayyacina, 'Yar uwata kanta dukta lalace kamar itace cikin matsalar. Innaro kam ciwon gwaggo Safiyya ne ya d'auke hankalinta, duk da dai su Abba sun mata bayanin kawo kud'in nawa, amma cikin halin ko in kula tace su basu kawai, idan sun barni agidan kuwa najawo musu abin kunyar dayafi nabaya, harma tashafi sauran kannena suk'i auruwa tamkar ni. Wannan furuci ya Sosa zuciyar abbanmu, amma saiya danne saboda girman mahaifiya. An sallamo gwaggo Safiyya da kwana biyu jikina ya birkice nima, dole aka kwasheni aka kai asibiti..... ********* A 6angaren sarki kuwa bayan tafiyar Galadima da kansa yazo masarautar gagara badau, an masa tarba ta girmamawa domin shid'in babban abokine ga kakansu Galadima wato (marigayi sarki Abubakar na lll). Mama Fulani kanta in kunga yanda take girmama sarki (Abdul'fatah idris) saikusha mamaki Ku d'auka ba itace mai ji da kanta d'innanba da tsantsar nuna sarauta(gaba da gabanta yo🥴). Sarki bai 6ata lokaciba ya sanar musu abinda yazo dashi, ganin tsantsar farinciki nayi ga mafi yawan jama'ar gidan, dan hukuncin sarki Abdul'fatah yamusu dai-dai, koba komai an k'ask'antar da Galadima d'in, Wanda yadace ace an sama masa d'iyar wani mashahurin sarki ya aura, kodan sarautar da ake da yak'inin shine yakama ta ya gada. Murmushi papi yayi, saboda ganin farinciki zancensa a fuskokin wasunsu, yasan tabbas dawata manufa suke wannan farinciki, amma hakan bai damesa ba, domin shi da k'yak'yk'yawar niyya yayi. maganar sarauta kuwa sune suke ganin bazai iyaba saida wata d'iyar babban sarki, amma shi yanada yak'inin ko d'iyar shugaban talakawan duniya koda baiwace agidan Galadima ya aura sarauta ta ALLAH Ce. Daga baya ya tsara musu yanda yakeso Neman auren ya kasance, bawai zasuje musu da rigar mulki baneba, yanason suje amatsayin talakawa domin ganin tarbar dazasu samu daga iyayen yarinyar, daganan zai gwada yak'inin tarbiyar gidan da mutuncin iyayenta. A masarautar sarki ya kwana, washe gari sukayi shigar talakawa shida sarki jalaludden k'anin mahaifin Galadima, sai wazirin papi dana sarki, saikuma k'annen mahaifin Galadima biyu sannan aka sami tsohuwar mota suka tafi aciki bisa jagorancin wani dogari da sarki yasa yamasa binciken gidansu munaya. Abinda basuyi zatoba shi suka samu, domin tarba ta mutunci da girmamawa suka samu dagasu Abba, duk da suna kallonsu talakawa fitik harma da yak'inin sun fisu komai. Hakan ya burge sarki Absul'fatah (papi) shi kansa sarki jalaludden lamarin ya masa dad'i. Sun bada kud'in gaisuwar farko data biyu naira subu 30 kacal. Sai bayan tafiyarsu sannan su Abba sukaita mamakin kansu anya mutanen bada wani siddabaru sukazo musuba? Yazama ayi basu sansuba amma suzo su kar6i auren 'yarsu? sukuma su basu babu musu kamar sun gaji da ita. (Niko nace kwarjinin sarauta suka muku abba😜😂). Can kuma dasu sarki suka tafi sunata yabawa suma, sarki Absul'fatah dad'i dukya gama cikasa, lallai Galadima yasamu tsatson daya dad'e yana masa fata da addu'ar samu. Momma koda papi yakira yamata bayanin bataji komaiba, saima addu'a data masa da kuma nuna farin cikinta akan lamarin, koba komai zataga auren Galadiman ta, amma saida tayi hawaye data tuna za ayi auren Galadima babu mahaifinsa, kamar yanda akayi na Haneefa (Aunty Mimi). Data sanarma Abie saiya fad'ad'a murmuahinsa, yayinda hawaye ke zirara ta gefen idanunsa, ALLAH sarki iko da falala, tun yaronsa na shekara 5 a duniya yake a wannan halin, gashi har zaiyi aure, yagodema ALLAH da wannan jarabawa shikam. A satin papi yaje India ma da kansa, yaduba jikin Abie dakuma maganar auren Galadima dayayi musu, nanma saida Abie yay hawaye, amma sarki Absul'fatah yayta masa nasihar yawan hak'uri da kar6ar k'addara, ya nuna masa sunada yak'inin zaici ribar can. Abie yana son surukinsa kuma aminin mahaifinsa sosai, dan duk lokacin dazaizo dubashi da irin salon nasihar dazai masa wadda zai k'ara tasirantar da imani a zuciyarsa. Galadima kuwa sai wani basarwa yakeyi irin shifa abin bai d'ad'ashi da k'asaba, kuma bayason abin, aurenma dole za ai masa, haka yaytaima Abie korafi yana shagwa6a. Murmushi Abie yay tayi yana lallaahinsa da idanun. Cikin tsokana sauban dake d'ayan gefen Abie shima yace “yaa Sam to kawai ni abani kana, kaga na huta da zuwa tad'i k'ofar gidan kowa”. Wata uwar harara Galadima ya maka masa, wadda tasaka Momma da auty Mimi da samha da jakadiya dariya, shi kansa Abie murmushine ya fad'ad'a afuskarsa.............✍🏼 Wannan shine yafaru 6angaren Galadima munaya bata saniba. Guys kuje zuwa kawai, k'ila zuwa dare kujini da bonus⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ ALLAH yabama munaya lafiya. Barka da juma'a.😄✋🏻 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣7⃣ .........Cikeda girmamawa yace, “Ranka ya dad'e barka da dare?”. “barkan ka dai Muhammad. dama kashigo k'asar kenan?”. Gabansa yad'an fad'i, danshifa yama manta mai martaba baisan yazo k'asarba, dakiyar dole ya aro yace, “wlhy kuwa nashigo d'azun yin wani aiki, amma gobema idan ALLAH ya kaimu zan koma”. “tofa, gobe gobe? kuma gashi inason ganinka a goben”. d'an jimm yayi, irin tamkar baisan komaiba, cikeda shakku yace, “ranka ya dad'e lafiya dai ko?”. “lafiya k'alau, wata muhimmiyar magana nakeson muyine”. “to shikenan, zanshigo insha ALLAH ”. “to madalla saina ganka”. Dafe kai Galadima yayi yana mamakin kansa, anya kuwa baima kansa d'aurin gorobo? koda yake idanfa yayi hak'uri shekara 1 ne ko 2 kacal, inma komai yafito kafin cikar shekarar zai sawwak'a matane, yad'an murmusa sannan yakoma ya kwanta abinsa cikeda tunani barkatai. ★★★★★ Rashin reply d'in Galadima ya dameni, haka dai naita danne zuciyata dankar innarmu da Munubiya su fahimta, nacigaba da harkokina tamkar banida wata damuwa a zuciya, saima sallar dare damuka fara dagewa da tashi nida Munubiya, gakuma azumin damuka tashi dashi yau litinin. Duk da innarmu ta fahimci inada damuwa batacemin uffanba, saidai tausayina na damun zuciyarta, tana dannewane kawai. Munubiya kam tsaf tagama fahimta ta, amma itama saita nuna bata fahimci komaiba, taje tasamu innarmu da maganar son a d'aga bikinta again. “munubiya ba wannan yakamata muyiba, addu'a yakamata muyima 'Yar uwarki, idan da rabo saikiga ALLAH ya kawo mata miji a cikin watanni 2nan dasuka rage kinji. nima nasan tana acikin damuwa, amma tana dannewa a zuciyarta saboda farin cikinmu. addu'ar dazamu mata itace tsantsar k'aunarta a garemu”. “shikenan innarmu, insha ALLAH zamu kuma dagewa da fad'ama ALLAH, itama ALLAH ya kawo mata ta hanyar da batayi zatoba, ya sakanka mata fiyeda sadaukarwar datayi, innarmu nasan sadaukarwar da 'Yar uwata tayine yasakata a wannan halin, ta sadaukar da farincikinta saboda ni, mizanyi na biyata nikam”. Murmushi innarmu tayi, tace, “addu'a”. ★★★★★ Washe gari yatashi ya shirin tafiya masarautar su Momma, Harun yakira yace ya nema masa ticket. Cikeda mamaki Harun yace, “yaushe kashigo k'asar Galadima?”. K'aramin tsaki yaja, dan shifa yama manta Harun baisan da zuwansa ba, Link d'in hannun rigar milk d'in shaddarsa yake k'okarin sakawa, cikeda dakiya yace, “jiya nazo da daddare, kuma inagama yau zan koma”. “tofa, amma baka cikin masarauta?”. “no a hotel Na sauka”. “ok barato a nema ticket d'in, sai muzo mu d'aukeka”. “karka damu harun, banason kowa yasan nazoma, muhad'u dakai kawai a airport ”. Koda suka yanke wayar sai yaja tsaki, gaba d'aya yakoma mak'aryaci, abinda yatsana arayuwarsa fiye da komai kenan (k'arya) amma sai gashi shi yana zundumata, “Astagafurullh” yashiga maimaitawa a zuciyarsa. Tsaf yafito cikin shadda milk color (nakula yana k'aunar milk) d'inkin rigar 3quarter, harda su hula, yayi k'yau sosai, yafito ainahin sa na cikakken bahaushe kuma basarake, ya fesa turaraensa Na kullum, komai nasa dayazo dashi ya had'a a waje d'aya. sannan yakashe kayan wutar bedroom d'in. Afalo ya iske Muftahu zaune yana jiransa, yad'anyi mamaki amma sai bai nunaba, yabashi hannu suka gaisa. Muftahu yace, “zaka dawo ta nan kenan?”.. Kai Galadima yad'aga alamar a'a, sannan yanufi kayan wutar falon yafara kashewa. saida yagama komai sannan ya kalli Muftahu alamar suje. Murmushi kawai Muftahu yayi, danya lura yau miskilawanne aka. Sun isa airport, lokacin shima harun harya je, mamakine ya kama harun Dan ganin Galadima tare da Muftahu, shima yanzu yana mamakin yanda Muftahu ke kuma kusanta kanshi da Galadima, baice komaiba yabashi hannu suka gaisa kamar yanda yabama Galadima. Harun yanason suyi magana da Galadima amma ga Muftahu a wajen, sai kawai yashare akan sayi a waya kawai. Basu wani dad'e a airport d'inba jirgin su Galadima yatashi. ★★★★ Yau hankalin kowa a tashe yake agidanmu saboda gwaggo Safiyya da aka kawo batada lafiya, dayake ba'anan kusa damu take aureba, tanacan wani gari daban, tun lokacin bikinsu yaa Hameed tamasu Abba complain akan batajin dad'i, amma kunsan maza darashin d'aukar Abu serious, sai basu maida hankalinsuba. Ita kuma kunya tahanata kuma musu maganar, har aka gama biki ta tafi, ashe baiwar ALLAH ciwo nata cin jikinta babu Wanda yasani, tun tanayi a tsitsaye har takai ga kwanciya, yaranta sun kaita asibiti amma basuga wani canjiba, hakanne yasa suka maidota gida, Dan aganinsu dai su Abba sunfi mahaifinsu k'arfi. Aiko suna isowa babu 6ata lokaci aka wuce da ita asibiti. Dan danan aka fara bata taimakon gaggawa. Muda innarmu ne kawai da innaro a asibitin, amma matan gidanmu babu wace tabimu, kusan mudasu baba k'arami muketa shiga da fita a asibitin dan ganin komai ya dai-daita. Kusan yamma saigasu Safara'u lokacin ma gwaggo Safiyya tana barci, yaranta duksunyi jigum-jigum da innaro saboda tashin hankalin dasuke ciki. Har dare ba'abar kowa yashiga wajen taba, sai su Dady kawai, ganin dare yayi akace mu muje gida kawai. Haka muka tafi akabar innaro da aunty habiba d'iyar gwaggo safiyyar ta uku, itama tayi aure amma tafito, yanzu zawarci takeyi. saikuma yaa Anas da aka barmusu saboda ko wani Abu zai taso. ★★★ Tunda yafito daga jirgi ya hango tawagar masarautar kakannin nasa, yasan tarbarsa sukazoyi, inhar zaishigo haka sukeyo gayyar tarbarsa, saikace wani bak'o daban, gefe yayi da fuskarsa dankarsu gansa, sashen motocin da akan d'auka drop ya nufa, duk manyan motocine da aka tanada dama domin irinsu, d'aya yabud'e da Kansa yashige da sauri, alamar yayma driver d'in suje. Tacikin glass yake kallonsu yana murmushi, yanda suketa d'aga kai nason hangosa, suna fita daga airport d'in ya kwantar da kansa ajikin seat ya lumshe idanunsa yana tunanin wane hukunci mai martaba zai yanke akan maganar, shin ya amincene? Kokuwa?. Driver yace, “oga ina muka nufa?”. Bai bud'e idonsaba kuma bai d'agoba, yace “gidan sarki”. Ta madubi driver n ya kallesa, “yalla6ai ko kaine ma dai akazo tarba daga masarauta?”. Murmushi kawai yayi batareda yace komaiba. Jin bai amsaba sai driver yakama bakinsa ya tauke shima. Ganin shine yasa dogarai suka bari aka shigar dashi har cikin masarauta, tunda yafito bayi da hadimai keta zubewa suna kwasar gaisuwa, hannu kawai yake d'aga musu, fuskarsa ad'an sake take, bai d'aureba baikumayi murmushi ko dariya ba kai tsaye. Tuni an kar6i kayansa an nufi sashin inno dasu, shikuma yanufi fada, Dan yasan yanzu Sarki suna fadanci. Cike fadar take da 'yan majalissar Sarki anata fadanci, bayan an masa iso yashiga da sallama, nanfa dogarai suka fara zuba masa kirari. Hannu kawai ya d'aga musu ya rissina yana mik'a gaisuwa ga Sarki. Sarki da fuskarsa tacika da fara'ar ganin jikan nasa ya amsa cikin lumshe idanu. Nan dogarai suka d'au da fad'in “sarki ya amsa maka sarkin gagara badau na gobe, an gaida magajin sarki, galadiman gagara badau, ALLAH yabaka zamani irinna sarki gagara badau. Galadima Yakuma rissinawa ya mik'a gaisuwa ga 'yan majissar sarki, suma cikeda fara'a suka amsa, kowa yasan irin tsantsar k'aunar da sarki kema jikan nasa a masarautar. Atake anan sarki ya sallami kowa, fadanci yatashi saikuma gobe idan ALLAH ya kaimu, yau yanada ganawa ta musamman da jikansa. Haka kowa yatashi yana musu addu'ar kasancewa cikin aminci. Tareda Galadima sarki yashiga cikin gidansa, hannunsa Na rik'e da Na Galadima, ba sabon Abu bane hakan a masarautar, duk Wanda yakwana yatashi acikinta yasan matsayin Galadima azukatan masu masarautar. Akatafaren falon sarki suka yada zango, babu dad'ewa da shigowarsu saiga jakadiya da kuyangi uku, kowanne d'aukeda babban tire, bayan sun dire komai suka zube suna kwasar gaisuwa wa sarki, sannan suka gaida Galadima. Jakadiya ma ta rissina ta gaida Galadima damasa barka da zuwa masarautarsu. Bayan fitarsu Galadima yakuma risainawa a girmame ya gaida sarki kakansa. Cike da murmushi sarki ya amsa yana kamo hannunsa, “Muhammad Sameer! kana lafiya”. “Alhmdllh ranka ya dad'e”. “Masha ALLAH, ya kabaromin Zeenah ta da jikin babanka da 'yan uwanka kuma su Haneefa?”. “Momma lafiyarta lau, hakama jikin Abie Alhmdllh, suma su aunty mimin haka”. “to Alhmdllhi, ALLAH yacigaba da jagorantar lamuranku ya albarkaci rayuwarku ta gobe da jibin jibima”. Murmushi Galadima yayi yana amsawa da amin. Sarki da Galadima tare sukaci abinci, (tun yana k'arami dama idan yazo gidan hakance ke faruwa tsakaninsu) Sunci sun k'oshi sukayi hamdala ga ALLAH. babu wani 6ata lokaci sarki yashiga masa bayanin kiran nasa akan maganar da Fateema (mom) tazo masa da itane jiya, shima ya zauna yayi nazari yagane hakan shine dai-dai, Galadima ya auri Munaya. tur6une fuska Galadima yayi tamkar baisan komaiba, yace “ranka yadad'e ka gafarceni, ammafa ni bata minba ai”. Sarki yay murmushinsu Na manyan k'asaitattun masu ji da mulki, “basai tayi makaba Muhammad, domin sanda Na aurama babanka Zeenah itama bai mataba, amma saboda biyayya dakuma tausayin d'iyar 'Yar uwarta ta amince tamin biyayya, to kaima hakan nakeso gareka, ka amsamin da to kawai saimu zauna lafiya, kasan magana biyu ba halina baceba ko”. Jinjina kai Galadima yayi yana kuma tankwashe k'afarsa, cikeda girmamawa yace “ALLAH ya huci zuciyarka ranka ya dad'e, Na amince da za6inka, ALLAH yabani ikon rik'ewa”. Cike da tsantsar farinciki Mai martaba ya rik'o hannun Galadima, “Muhammad ALLAH shiyi maka albarka, ya tsareka dadukkan sharri, ALLAH yabama mahaifinka lafiya kaji”. “amin ranka ya dad'e, ngd sosai ”. Daga nan hira suka cigaba dayi cikin tsantsar soyayya da k'aunar juna, kowanne yanajin d'an uwansa sosaih a ransa. Kusan atare suka yini, inno tun tana zuba idon shigowar Galadima harta hak'ura. Galadima bai shigo wajenta ba sai bayan sallar magriba. Tundaga k'ofar sashenta hadimai keta kwasar gaisuwa, tuni labarin tahowarsa ta iske inno, hakan yasa ta k'imtsa da k'yau, ta sallami bayinta masu mata hidima. Fuskarsa d'auke da k'ayataccen murmushi ya k'araso falon, bai zauna ko inaba sai jikin kakarsa, oh my sweet inno I miss you so much wlhy”. Kunnensa tad'anja kad'an, cikeda tsokana tace “miskili kafi mahaukaci ban haushi, aini harna fara shirin yo bikonka daga turakar mai martaba”. Yayi 'Yar dariya yana fad'in “tuba nake ginbiyar papi”. “ja'irin kaya, bazaka canjaba dai? ya kabaro iyayen naka da 'yan uwanka?”. “kowa lafiya lau ranki ya dad'e”. “to Alhmdllhi ”. Nanma hirarce ta 6alle tsakanin kaka da jikanta, kan mace me nanma an cika masa gaba da kayan itatuwa, shikuma yana zubama inno shagwa6ar daya saba tana biye masa. Masu jiran Galadima kuwa a airport saida sukaga kowa yagama fita ajirgi babushi sannan wani dogari yakira sarkin fada yake sanar dashi sufa basuga Galadima ba. Sarkin fada yace “yo kunacan kuna shashanci yaza'ayi Ku gansa, shi harma sun shige cikin gida da sarki ”. 'yan uwansa ya sanarmawa suka tattaro suka dawo masarautar.🤣 Dole a nan masarautar ya kwana, washe gari ya zagaya duka sashen sauran matan sarki ya gaidasu a mutunce. suma dai sunmasa tarbar mutunci kamar yanda suka saba, duk da dai taciki Na ciki. Sannan sai sassan iyayensa yayun momma da k'annenta, dukda dai bako ina yashigaba. Yanzunma tare sukayi karin kumallo da maimartaba, sannan suka fita fada tare, da Galadima akayi fadanci yau, yana gefen adalin kakansa. Washe gari da safe ya tattara inasa-inasa ya cane India, yabar tsofin da kewarsa, shima yatafi yana kewarsu. ******** Gwaggo Safiyya tacigaba da samun kulawa sosai, dukda dai tanad'an jin jiki, kullum matan gidanmu sukanzo sau d'aya, muma dai makaranta tasa bama yini a asibitin, amma kullum da safe mukanzo mu kuma dawo da yamma. Matan gidanmu kam jarabar innaro tasakasu k'ok'arin zuwa kullum, dan tace wlhy duk Wanda bata zuwa saitayi Dana sanin saninta. Wannan furuci ya d'an tsoratasu, dan kowa agidan yasan wacece innaro, idan kaga mutuncinku ya d'ore to kana cinna mata 'yan canji ta k'ark'ashin k'asane🙊, amma kana hanata gobe bazai hana ta karta maka rashin m ba🤣. (Ho innaro mu ta mutunci🤸🏻‍♀, ina yinki over ginbiyar Malam faruku😜🙊) ⛹🏻‍♀ Abin yafara tsoratani ganin har sati 1 dayin maganarmu dasu Galadima amma babuko labarinsu, tun ina saran yau gobe har na daina lissafin ma, ganin zan saka kaina a damuwa nacirema zancen a raina gaba d'aya, domin Na gama fahimtar maganar Galadima da abokinsa k'aryace, maybe ma mafarki nayi naketa shirmena kawai. A tsaitsaye damuwa tafara ramar dani a tsaye, sai idanuwa da dogon hanci. Tun ina daurewa har Abu yaso yaci tura, ciwon kai Dana k'irji suka fara zama abokaina. Ranar data kama sati biyu cif saiga bak'i su Abba sunyi, babu Wanda yasan daga ina suke, kuma su Abba basuma kowa bayanin komaiba dangane da bak'in. saida sukayi kwanaki uku da zuwa sannan naji wai wanine yakawo kud'in aurena yana son abama d'ansa. Lamarin yabama kowa mamaki, nanfa 'yan gidanmu suka hau dariyar mugunta wai kwantai dai ya tabbata kenan. Gugar zanar dasuke tayine ya fusata innarmu, tasakama Abba kuka akan bata aminceba, yaza'ayi su d'auki aurena subama mutumin dabasu saniba, idan su sun gaji dani itafa tanason kayarta. Lallashi duniya Abba yayi dan innarmu ta fahimta amma Sam tak'i saurararsa, wannan ne karon farko da yaga tsantsar fushinta. Yarasa yazai mata, dan shima lamarin Na damunsa, yarasa minene yasakashi amincewa yabada auren d'iyartasa ga mutanen?, shi dai kawai tsohon yamasa kwarjinine wlhy, dan jiyay ko kad'an bazai iya musa masaba. dukda talakawane kamarsa, harma yana ganin yafisu abubuwa da yawa. Lamarifa yayi tsamari a d'an tsakaninnan a gidanmu, dan innarmu takasa kwantar da hankalinta, hakama abbanmu, yayinda 'yan gidanmu sukejin Dad'i kamar su had'a fati. Nikuwa uwar gayya ai ba'a magana ma, nakira number Galadima yafi sau 200 amma tak'i shiga ko sau d'aya, lokaci guda nagama fita hayyacina, 'Yar uwata kanta dukta lalace kamar itace cikin matsalar. Innaro kam ciwon gwaggo Safiyya ne ya d'auke hankalinta, duk da dai su Abba sun mata bayanin kawo kud'in nawa, amma cikin halin ko in kula tace su basu kawai, idan sun barni agidan kuwa najawo musu abin kunyar dayafi nabaya, harma tashafi sauran kannena suk'i auruwa tamkar ni. Wannan furuci ya Sosa zuciyar abbanmu, amma saiya danne saboda girman mahaifiya. An sallamo gwaggo Safiyya da kwana biyu jikina ya birkice nima, dole aka kwasheni aka kai asibiti..... ********* A 6angaren sarki kuwa bayan tafiyar Galadima da kansa yazo masarautar gagara badau, an masa tarba ta girmamawa domin shid'in babban abokine ga kakansu Galadima wato (marigayi sarki Abubakar na lll). Mama Fulani kanta in kunga yanda take girmama sarki (Abdul'fatah idris) saikusha mamaki Ku d'auka ba itace mai ji da kanta d'innanba da tsantsar nuna sarauta(gaba da gabanta yo🥴). Sarki bai 6ata lokaciba ya sanar musu abinda yazo dashi, ganin tsantsar farinciki nayi ga mafi yawan jama'ar gidan, dan hukuncin sarki Abdul'fatah yamusu dai-dai, koba komai an k'ask'antar da Galadima d'in, Wanda yadace ace an sama masa d'iyar wani mashahurin sarki ya aura, kodan sarautar da ake da yak'inin shine yakama ta ya gada. Murmushi papi yayi, saboda ganin farinciki zancensa a fuskokin wasunsu, yasan tabbas dawata manufa suke wannan farinciki, amma hakan bai damesa ba, domin shi da k'yak'yk'yawar niyya yayi. maganar sarauta kuwa sune suke ganin bazai iyaba saida wata d'iyar babban sarki, amma shi yanada yak'inin ko d'iyar shugaban talakawan duniya koda baiwace agidan Galadima ya aura sarauta ta ALLAH Ce. Daga baya ya tsara musu yanda yakeso Neman auren ya kasance, bawai zasuje musu da rigar mulki baneba, yanason suje amatsayin talakawa domin ganin tarbar dazasu samu daga iyayen yarinyar, daganan zai gwada yak'inin tarbiyar gidan da mutuncin iyayenta. A masarautar sarki ya kwana, washe gari sukayi shigar talakawa shida sarki jalaludden k'anin mahaifin Galadima, sai wazirin papi dana sarki, saikuma k'annen mahaifin Galadima biyu sannan aka sami tsohuwar mota suka tafi aciki bisa jagorancin wani dogari da sarki yasa yamasa binciken gidansu munaya. Abinda basuyi zatoba shi suka samu, domin tarba ta mutunci da girmamawa suka samu dagasu Abba, duk da suna kallonsu talakawa fitik harma da yak'inin sun fisu komai. Hakan ya burge sarki Absul'fatah (papi) shi kansa sarki jalaludden lamarin ya masa dad'i. Sun bada kud'in gaisuwar farko data biyu naira subu 30 kacal. Sai bayan tafiyarsu sannan su Abba sukaita mamakin kansu anya mutanen bada wani siddabaru sukazo musuba? Yazama ayi basu sansuba amma suzo su kar6i auren 'yarsu? sukuma su basu babu musu kamar sun gaji da ita. (Niko nace kwarjinin sarauta suka muku abba😜😂). Can kuma dasu sarki suka tafi sunata yabawa suma, sarki Absul'fatah dad'i dukya gama cikasa, lallai Galadima yasamu tsatson daya dad'e yana masa fata da addu'ar samu. Momma koda papi yakira yamata bayanin bataji komaiba, saima addu'a data masa da kuma nuna farin cikinta akan lamarin, koba komai zataga auren Galadiman ta, amma saida tayi hawaye data tuna za ayi auren Galadima babu mahaifinsa, kamar yanda akayi na Haneefa (Aunty Mimi). Data sanarma Abie saiya fad'ad'a murmuahinsa, yayinda hawaye ke zirara ta gefen idanunsa, ALLAH sarki iko da falala, tun yaronsa na shekara 5 a duniya yake a wannan halin, gashi har zaiyi aure, yagodema ALLAH da wannan jarabawa shikam. A satin papi yaje India ma da kansa, yaduba jikin Abie dakuma maganar auren Galadima dayayi musu, nanma saida Abie yay hawaye, amma sarki Absul'fatah yayta masa nasihar yawan hak'uri da kar6ar k'addara, ya nuna masa sunada yak'inin zaici ribar can. Abie yana son surukinsa kuma aminin mahaifinsa sosai, dan duk lokacin dazaizo dubashi da irin salon nasihar dazai masa wadda zai k'ara tasirantar da imani a zuciyarsa. Galadima kuwa sai wani basarwa yakeyi irin shifa abin bai d'ad'ashi da k'asaba, kuma bayason abin, aurenma dole za ai masa, haka yaytaima Abie korafi yana shagwa6a. Murmushi Abie yay tayi yana lallaahinsa da idanun. Cikin tsokana sauban dake d'ayan gefen Abie shima yace “yaa Sam to kawai ni abani kana, kaga na huta da zuwa tad'i k'ofar gidan kowa”. Wata uwar harara Galadima ya maka masa, wadda tasaka Momma da auty Mimi da samha da jakadiya dariya, shi kansa Abie murmushine ya fad'ad'a afuskarsa.............✍🏼 Wannan shine yafaru 6angaren Galadima munaya bata saniba. Guys kuje zuwa kawai, k'ila zuwa dare kujini da bonus⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ ALLAH yabama munaya lafiya. Barka da juma'a.😄✋🏻 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣8⃣ ..........A Asibiti gado suka bani, sunata fad'an yanda jinina ya hau sama, su mamakima suke yi 'yar k'aramar yarinya dani amma inada hawanjini, shin miyayi zafi haka?. Su Abba dai kasa cewa komai sukayi, dan su kansu abin na yata6a zuciyarsu. Wannan karonma Mama Rabi'a da Munubiya ne suka kwana a wajena, washe gari da yamma saiga 'yan gidanmu wai sunzo dubani, bamuyi mamakiba Dan munsan ba domin ALLAH sukazoba, kawai sunzo ganin kwafne. Duk suncika d'akin da surutu akan wai suna mamakin miya samin hawan jini?. daga mama Rabi'a har Munubiya babu wanda yabasu amsa. Doctor ne yashigo yace sud'an ragu wasu su fita baranda dan ALLAH, duk fita sukayi harda mama Rabi'a aka barmu iya mu yaran kawai, dansu Fiddausi duk hadasu akazo. Ina daga kwance kan gado ina sauraren hirar dasukeyi, wai safara'u da Halimatu ne sukaje gidan su Siyama tai tamusu yatsina da d'aukar kai, saikace ba 'yan uwanta ba, mijinta yadawo sukayi shigewarsu suka barsu afalo har yamma sannan suka fito, mai makon tabasu hak'uri sai cewa tayi wai dama basu tafiba🤣. Wannan abun daya faru shine yajawo rigima a gidanmu jiya da daddare, har saida su Abba suka tsawatar. Murmushi kawai nayi Na gyara kwanciyata, a zuciyata ina fad'in maganinku ai, baku masu dangiba..........gabana yafad'i, saboda jin tamkar k'amshin turarensa. da sauri Na d'ago kai saboda jin su Fauziyya ma sunyi tsit daga surutun dasukeyi suna kallon bayanmu. Wani yaam naji a raina domin ganin Galadima da tawagar dogaransa, sai wani dake gefensa amma ba muftahu bane, (Harun ne). Sanye cikin k'ananun kaya wad'anda suka fidda ainahin k'irarsa ta cikakken namiji, fuskarnan kamar kullum babu walwala. Mu 4 ne kawai a d'akin, dan haka yana tsaye a gadon farko da alama tanbayoyi yakema matar dake jiyya a gadon. gani nai yasaki wani guntun murmushin gefen baki sannan ya kalli harun, bansan miya cemasaba nagadai yabaro wajen yana tunkaro gado Na biyu. A hankali Na lumshe idanuna wani Abu Na tsikarar zuciyata mai kama da tsoro da rud'ani. Sauran 'yan uwana kam sun zuba masa idanu tamkar zasu cinyesa, kowacce takasa furta komai a fili saida a zuciyarta take tattaunawa da yaba Galadima d'in. Annanma yayi kusan mintuna hud'u sannan ya tunkaro gadon takusa damu, dan nice ta k'arshe. duk da akusa damu yake banajin miyake fad'a, saidai motsin la66ansa kawai nake gani, tabbas Galadima naji da Girman kai da mulki, kallo d'aya zaka masa ka tabbatar da tsantsar sarauta da mulki dake yawo a jinin jikinsa....... tunda naga yanufo inda nake sai kawai narufe idanuna gaba d'aya. Su Munubiya duk suka risina suna gaidashi. Hannu kawai ya d'aga musu yamatso jikin gadon danake. Tsantsar mamakine ya bayyana a fuskarsa, yad'anyi kamar zai nunani da hannu saiya kuma fasa, su safara'u kam duk sun zubo mana idanu suga yanda za'a kwashe. Munubiya ce cikin k'arfin hali tace “Munaya ki tashi ana miki magana fa”. daka ganta kasan a tsorace take maganar. Shima juyowa yayi ya kalli Munubiyar domin jin kuma Muryata, maganar Muftahu ta fad'o masa arai dayace yaran twins ne, kuma ba'a iya banbancesu. Suma Kansu dogaran NASA da Harun duk sunyi tsuru suna kallonmu, domin babu wanda baiga jaridarba a wancan lokacin. Maganar sace tasaka kowa maida hankali a kansa, nidai har yanzun idona arufe suke, cikin basarwa da nuna halin ko in kula yace, “ya jiki?”. tamkar bayaso haka yayi maganar. Nima cikin dakiya da shariyar kamar yanda yamin nabud'e idona nace “Alhmdllh”. Kamar yanda yake tambayar kowa nima haka ya tambayeni miye matsalata?. Na d'a6e baki sannan nace “masassara”. Harun ya kalla, danshi baima fahimci minake nufiba. Murmushi harun yayi, danya fahimci bai ganeba, cikin gyara tsayuwa yace “tana nufin fever”. Caraf fiddausi tace, “ranka yadad'e k'arya take hawan jinine”. Juyowa yayi ya kalli fiddausin da fararen idanunsa wad'anda suka nemi zautata, bai Ce komaiba ya janye ya maida kan Munubiya, “Sister naga drugs d'innan?”. yafad'a kamar anmasa dole. Ko kad'an Munubiya bataji maiya fad'aba, dan a saman la66ansa yayi maganar, tana shirin sake tambayarsa d'aya daga cikin dogaran ya maimaita mata a tsawace. Nikaina saida Na bud'e ido saboda tsawar, Na bankama dogarin harara ina magana k'asa-k'asa yan da babu mai jina, kajimin shegen dogari, dan tace batajiba zakawani daka mata tsawa?, shi mizaisa bazai bud'e baki yayi magana yanda kowa zaijiba? Mutum sai azabar Girman kai mtsoww, koma R bai iyaba. Duk maganar danake la66ana ne kawai ke motsawa, shikuma idon nasa nakan la66ana, dukda duba kwalin drugs dayakeyi, tsaf ya karanci duk maganar danakeyi. yayi wani munafukin guntun murmushi yana mik'ama Munubiya magungunan. Juyawa yayi yama Harun magana, sannan ya juyo ya kalleni yana fad'in “ALLAH yak'ara lafiya”. Harara Na zuba masa batare da tunanin zai ganiba, amma sai caraf muka had'a idanu. Janye idanunsa yayi a kaina yajuya yabar wajen yana cije lips d'insa da mamakin yarinyar nan da batada tsoro. su Safara'u Na zuba masa godiya, duk da zukatansu Na mamakin yanda yanuna tamkarma bai sanmu ba. Ko kallonsu baiyiba ya d'aga musu hannu, sukuma sunyine dama danya tanka musu. Harun ya tambayi Munubiya wane doctor ne ke dubani?. Ta Sanar masa. Addu'a yaymin sannan yabar wajen shima. Lumshe idanuna nayi zuciyata Na kaikawo, yanda Galadima yayi, saiya kuma tabbatar min da mafarki dai nayi kenan, bawai gaba da gaba ba yace muyi Auren Contract ba kenan. Innalillhi, mike shirin faruwa danine ni Hussaina, hawayen dasuke neman zubomin nai k'ok'arin had'iyewa, Munubiya kanta tashiga kogin mamakin yanda Galadima yay tamkar ma komai baita6a faruwaba, shin kodai shi baiga abinda yafaru a jaridar baneba?.... Batada mai bata amsa, su safara'u ma magana suketayi k'asa-k'asa a tsakaninsu, alokacinne kuma matan gidanmu suka shigo. Mamansu yaa hameed take tambayar wai wananan bashine Galadima ba na jikin jaridar nan?. “wlhy shine kuwa mama”. cewar Fiddausi. Haleematu ta kar6e da fad'in “mama kinga yanda ya nuna kuwa? tamkar ma bai gane su twins ba balle ya nuna yama San abinda yafaru a bayabaya tsakaninsu”. Murmushin mugunta mamansu ya hameed tayi, “yo ai dama saboda irin haka ake cewa Ku kare mutuncin kanku, danshi namiji komi yayi adone, sannan shi d'an manyan mutanene, ko kallonsa da abin babu mai sakeyi, amma Ku gashi har ana fasa aure, kamun kai dai dad'i gareshi ai dama, kum.......” Shigowar doctor tasaka maman su yaa hameed yin shiru, korarsu yayi gaba d'aya, yace subarni Na huta. Basuso hakanba, dan shirya cin zarafinmu maman yaa hameed tayi. Daganan gida suka wuce suna 'yan gulmace-gumacensu da dariyar mugunta. ★★★★★ Galadima kuwa yana gama zagaye-zagayensa a asibitin na duba marasa lafiya gida suka wuce. Bayanin doctor yabashi mamaki, wai wannan 'yar yarinyar keda hawan jini, itako miyayi zafi haka a rayuwarta”. wani sashi na zuciyarsa yabasa amsa da (6atancin da akai muku). Lips d'insa ya cije yana jan dogon tsaki, shikad'ai yasan burin daya d'auka akan dukkan Wanda yasamu da hannu a wannan lamarin. Sun biya birnin gayu plaza yaga komai yana tafiya dai-dai, daga nan suka koma masarauta. ★★★★ Nima a ranar da daddare aka sallamoni, nadawo gida nacigaba da shan Magani, yayinda biki keta gaba towa kuma. Har yanzu innarmu tana cikin damuwa dani kaina akan zancen aurena daba asan taka maimai angoba. Zancen galadima kuwa ai tini na shareshi, dan nabarsa amatsayin mafarki nayi, musamman kuma dana bincika banga number wayan daya baniba, a wayata kuma tun randa na tura masa massege na gogeta dama gudun kar wani yagani. Yanda 'yan gidanmu suketa rawar kai akan bikin saran 'yan uwanmu innarmu batayi, bazama ka ta6a d'auka itama zata aurar da 'ya'ya har biyu baneba. Mama Rabi'a ce ke tsaye akan komai, sai aunty salamah datazo da magunguna ta d'id'd'irka mana, mu bamusan namiye ba, takumace mudinga sha, saikuma had'ad'd'en sabulun wanka da mai data had'a mana, ga wasu turare masu sirrin k'amshi, takuma gargad'emu daga yanzu muna saka hijjab duk inda zamuje da nik'af, domin fatarmu tasami nutsuwa kar rana ta maidamu gidan jiya. Ni dai dagani har munubiya da to kawai muke binta, kuma duk abinda tace muyi munayinsa. Abbanmu yakira mama Rabi'a yabata wasu kud'i akan tak'ara amana siyayyar kayan kitchen da 'yan uwa keyi, tunda ita innarmu bawasu dangi ne da itaba dazasu tara mata. Sosai tamasa godiya, sanan tasanarma innarmu, ko babu komai taji dad'i, harma tamasa godiya itama. Tafiya mama Rabi'a tayi da k'ud'in, washe gari suka Shiga kasuwa itada inna lami, kaya masu k'yau suka sissiya mana dai-dai gwargwadon k'arfinmu. aka adanasu gidan inna lami duka. *_kwanci tashi_* Babu wahala wajen ubangiji, yau gashi abinda kowa yake jira yazo, domin kuwa ankawo lefen Haleematu, gaskiya angonta yayi k'ok'ari, akwati 5 abinta, kuma kaya masha ALLAH, sai-dai hakan bai hana 'yan gidanmu gulmaba, washe gari kuma aka kawo kayan Safara'u da Fiddausi. Suma dai kam saidai mak'iyi, amma jikin maman safara'u yayi sanyi, dan gaskiya kayan sauran duk sunfi nata. Itama dai akwati biyarne, amma kayan cikine basukai na sauranba. Again washe gari saiga na Fauziyya da Munubiya, mama Rabi'a tasan komai dake wakana a gidanmu, dan haka suka dage sukaima Munubiya lefe na 'Yar gata, wlhy ba fariyaba lefenta yafi na kowa, ranar har kukan dad'i nayi, domin banyi zaton hakanba. itama dai fauziyya angonta yayi k'ok'ari gaskiya. Tuni hassadar matan gidanmu tafito fili suka fara yada habaici wai an aro kaya anzo ana musu burga, da anyi aure sai ake maidawa d'ai-d'ai. Dagamu har innarmu babu Wanda ya tanka musu, dan munsan yau dai mune aciki sune a kwana🤣🥴. Rashin kawo nawa lefen kuwa ko a kwalar rigata bai dameniba, dan bama sanin mijin nayiba balle nadamu dawani lefen banza. saima Munubiya ce harda kukanta rurus akan wai saidai araba mana kayanta mu biyu. Nifa dariyama tabani wlhy. Ganin ni babu lefe yasaka su baba k'arami siyomin kaya masu k'yau na fitar biki har kala 10, aka d'inka min, sai takalma da bags da veils masu k'yau suma. Habaici dai kam munshashi wa su innaro da matan gidanmu, danma ita innaro gwaggo Safiyya na hanata ne, da bamu san tijarar dazata zubarba a ranar kam. A haka aka shiga satin biki, mu bamu wani gayyaci k'awayeba, daga Bilkisu sai su Ayusher, ashe Ayusher ta buga invitation na k'awaye suka raba itada Bilkisu bamu saniba. Abin mamaki ranar kamu sai ganin k'awayenmu mukayi harna secondary. munji dad'in hakan sosai kuwa. A ranar kamun saiga wasu mata hud'u sunzo wai dangin miji nane, su mama Rabi'a sukayi musu tarba ta mutunci, ba a nuna musu komaiba kuma, dukda a yanayin shigar talauci da sukazo, saidai zund'e da gulma irinta 'yan biki. Matan gidanmu kam komai ya kaimusu dai-dai, sai dariya da yada magana a kaikaice sukeyi. Da aka kaisu su gaisa da innaro taita musu yatsine-yatsine, harda tanbayarsu waisu garinsu ba'a lefene? dabasu kawoma jikartaba?. Basuce komaiba sai murmushi kawai da sukayi. Washe gari kuma akayi k'unshi, mudai namu aunty Salamah ce tamana, tana tsaye akan komai namu tamkar yayarmu ciki d'aya. A ranar kuma akaje a kaima sauran amaren jere, harda Munubiya, amma ni banda ni, tunda ba'asan ina za'aje ayiba. Aranarma Munubiya tayi kuka, nidai ina k'ok'arin danne zuciyata, saboda nabama innarmu kwarin gwuywa karta tada hankalinta. Aiko Alhmdllh ta dake tamkar komai baya damunta, tashige cikin abokan arzik'inta sunata harkoki. kowanne 6angare yacika da dangin matan gidanmu, abin tamkar fariya, namu 6angarenne kawai keda sauk'in jama'a, hakama gidan innaro yacika da danginta da dangin kakanmu. Tunda aunty Salamah tagama yimana k'unshi da gyaran kai dana jiki sai muka nufo hanyar gida, saboda yaa marwan yazo neman Munubiya harsau biyu, sai kiran wayarta yake yana masifa saboda tare yake da abokansa. hakan yasa muka taho gida. Gashi Yau zamuyi sister's and brother's day, duk da dai saima da yamma. ★★★★★ Galadima dake zaune a makeken falon Ummu hasheem, yanata bin jerin akwatinan da kallo, ga wasu daga 'yan uwansa zazzaune sunata kuma kimtsa kayan, aunty Mimi ta kalleshi, “kunga zanma mantafa, my k'ani ina kayan dana baka kayo gaba dasune?”. Yatsine fusaka yad'anyi yana gyara zamansa, “nifa nama manta inda suke, shiyyasa nace bazan d'akkoba ai”. Wata uwar harara ta watsa masa tace, “lallai bakada kai yaro, bar ganin matarka za'a kaimawa, suka 6ata biyana zakayi ehe” Murmushin gefen baki yasaki yana lumshe idanu, cikeda k'asaitarsa yace, “Samha! jeki bedroom d'ina ki duba, maybe suna can“. “bama kada tabbas kenan?” cewar mom. Bud'e idanunsa yayi yana murmushi, “no mom insha ALLAH sunama can. ni yanzu kam kun sallameni natashi natafi? dan zansa aje a d'auko su Akash a airport ”. Ummu Hasheem tace “kaje kawai, dama dan kaga kayanne, tunda kuma kace komai yayi ai shikenan”. Mik'ewa yayi yana fad'in “thanks you Ummu, nabarku lafiya”. Tunda yasamu yay escape sai ya sauke ajiyar zuciya, shi dariyama suke bashi dagasu har su papi, su Dan basu san auren shekara d'aya bane dabasu dinga wannan rawar k'afarba, sun wani zauna sun had'a uban kayan lefe, yad'an ta6e bakinsa kawai yana nufar sashensa. Komai na gidan sarauta mai tsarine, dan haka kai lefen MUNAYA da suke shirin yima a tsare akayisa, (papi ne yace Subari sai yau ana gobe d'aurin aure sai akai, tunda gidan su munaya basusan kosu su wayeba). An tsara iya wad'anda zasu kai lefenne. Bayan an gama zuba akwatunan a wata farar mota mai k'yau sabuwa dal aka rufe, driver ne kawai zai shiga cikin motar. Sai kuma motoci 6 da aka zaba wad'an da zasu kai lefen. Motar farko dogaraine, ta biyu kuma kuyangi ne, sai guda biyu 'yan cikin gidansu Galadima ne su hud'u, ko wacce mota mutum biyu, sauran biyun kuma 'yan 6angaren masarautar su Momma, suma su hud'u, kowacce mota biyu. sai Samha datasa kuka saitaje taga matar Uncle Sam. Aunty mimi harta korata da zare mata idanu saiga Galadima motocin na niyar tashi. Da kansa yabud'e mata gaban motar da aka saka akwatinan yace tashiga nan, idan taje ta gaida masa matarsa. Cikeda d'oki tace zataji Uncle Sam, bazaka bada komai akai mataba. Kansa yad'an dafe dan yakula Samha na neman k'uresa, shikuma yafad'a mata maganarne domin yanason agaban jama'a yadinga yana tsantsar k'aunar Munaya, a bad'ini kuma suna zaman aurensu na contract, shiyyasa ko lefennan baiji tsadar kud'in saba yabud'e bakin aljihu aka zuba kaya masu azabar k'yau, gakuma kud'in da Mai martaba yabada shima, dakuma sauran k'annen mahaifinsa. Hannu yasaka a aljihunsa yana duba kozai samu wani Abu, amma babu komai sai wata chocolates guda biyu, wadda ya d'akkota ne zaiba khaleel d'azun yama manta, mik'ama Samha yayi yace “gashi kibata”. Da dariya samha ta kar6a tace “Uncle ta gode to”. Kansa kawai ya jinjina mata ya shirin barin wajen. motocin suna fita daga masarautar saiya sauke ajiyar zuciya kawai. ★★★★ Gidanmu ya cakud'e da hayaniyar da akasan gidan kowanne biki da ita, bare mu daya kasance har auren mutum 6, dukda sai gobene d'aurin aure kuwa, yara sunata wasansu da tsalle-tsalle. A jere motocin suka shigo cikin anguwar, jama'a sai binsu da kallo sukeyi, dai-dai k'ofar gidanmu driver daya san gidan yay parking. Babu Wanda yay mamaki a 'yan kawo lefe, domin kuwa dama labari ya karad'e masarautar cewar Galadima'yar talakawa zai aura. Dogarawa da kuyangi suka fara fitowa, sannan suka bud'e motor da akwatina suka suka fara fitarwa. Nanfa jama'ar anguwa sukayi cirko-cirko suna kallon ikon ALLAH dan ganin akwatinan da aketa fitarwa daga mota. Batare da neman isoba Kuyangin suka fara kwasar akwatinan suna shiga dasu gidanmu..............✍🏼 😂😂😂 Team innaro kufito mu caskale yau🙊🤸🏻‍♀ ⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ Asha weekend lafiya😅✋🏻 *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu👏🏻😭_* *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣8⃣ ..........A Asibiti gado suka bani, sunata fad'an yanda jinina ya hau sama, su mamakima suke yi 'yar k'aramar yarinya dani amma inada hawanjini, shin miyayi zafi haka?. Su Abba dai kasa cewa komai sukayi, dan su kansu abin na yata6a zuciyarsu. Wannan karonma Mama Rabi'a da Munubiya ne suka kwana a wajena, washe gari da yamma saiga 'yan gidanmu wai sunzo dubani, bamuyi mamakiba Dan munsan ba domin ALLAH sukazoba, kawai sunzo ganin kwafne. Duk suncika d'akin da surutu akan wai suna mamakin miya samin hawan jini?. daga mama Rabi'a har Munubiya babu wanda yabasu amsa. Doctor ne yashigo yace sud'an ragu wasu su fita baranda dan ALLAH, duk fita sukayi harda mama Rabi'a aka barmu iya mu yaran kawai, dansu Fiddausi duk hadasu akazo. Ina daga kwance kan gado ina sauraren hirar dasukeyi, wai safara'u da Halimatu ne sukaje gidan su Siyama tai tamusu yatsina da d'aukar kai, saikace ba 'yan uwanta ba, mijinta yadawo sukayi shigewarsu suka barsu afalo har yamma sannan suka fito, mai makon tabasu hak'uri sai cewa tayi wai dama basu tafiba🤣. Wannan abun daya faru shine yajawo rigima a gidanmu jiya da daddare, har saida su Abba suka tsawatar. Murmushi kawai nayi Na gyara kwanciyata, a zuciyata ina fad'in maganinku ai, baku masu dangiba..........gabana yafad'i, saboda jin tamkar k'amshin turarensa. da sauri Na d'ago kai saboda jin su Fauziyya ma sunyi tsit daga surutun dasukeyi suna kallon bayanmu. Wani yaam naji a raina domin ganin Galadima da tawagar dogaransa, sai wani dake gefensa amma ba muftahu bane, (Harun ne). Sanye cikin k'ananun kaya wad'anda suka fidda ainahin k'irarsa ta cikakken namiji, fuskarnan kamar kullum babu walwala. Mu 4 ne kawai a d'akin, dan haka yana tsaye a gadon farko da alama tanbayoyi yakema matar dake jiyya a gadon. gani nai yasaki wani guntun murmushin gefen baki sannan ya kalli harun, bansan miya cemasaba nagadai yabaro wajen yana tunkaro gado Na biyu. A hankali Na lumshe idanuna wani Abu Na tsikarar zuciyata mai kama da tsoro da rud'ani. Sauran 'yan uwana kam sun zuba masa idanu tamkar zasu cinyesa, kowacce takasa furta komai a fili saida a zuciyarta take tattaunawa da yaba Galadima d'in. Annanma yayi kusan mintuna hud'u sannan ya tunkaro gadon takusa damu, dan nice ta k'arshe. duk da akusa damu yake banajin miyake fad'a, saidai motsin la66ansa kawai nake gani, tabbas Galadima naji da Girman kai da mulki, kallo d'aya zaka masa ka tabbatar da tsantsar sarauta da mulki dake yawo a jinin jikinsa....... tunda naga yanufo inda nake sai kawai narufe idanuna gaba d'aya. Su Munubiya duk suka risina suna gaidashi. Hannu kawai ya d'aga musu yamatso jikin gadon danake. Tsantsar mamakine ya bayyana a fuskarsa, yad'anyi kamar zai nunani da hannu saiya kuma fasa, su safara'u kam duk sun zubo mana idanu suga yanda za'a kwashe. Munubiya ce cikin k'arfin hali tace “Munaya ki tashi ana miki magana fa”. daka ganta kasan a tsorace take maganar. Shima juyowa yayi ya kalli Munubiyar domin jin kuma Muryata, maganar Muftahu ta fad'o masa arai dayace yaran twins ne, kuma ba'a iya banbancesu. Suma Kansu dogaran NASA da Harun duk sunyi tsuru suna kallonmu, domin babu wanda baiga jaridarba a wancan lokacin. Maganar sace tasaka kowa maida hankali a kansa, nidai har yanzun idona arufe suke, cikin basarwa da nuna halin ko in kula yace, “ya jiki?”. tamkar bayaso haka yayi maganar. Nima cikin dakiya da shariyar kamar yanda yamin nabud'e idona nace “Alhmdllh”. Kamar yanda yake tambayar kowa nima haka ya tambayeni miye matsalata?. Na d'a6e baki sannan nace “masassara”. Harun ya kalla, danshi baima fahimci minake nufiba. Murmushi harun yayi, danya fahimci bai ganeba, cikin gyara tsayuwa yace “tana nufin fever”. Caraf fiddausi tace, “ranka yadad'e k'arya take hawan jinine”. Juyowa yayi ya kalli fiddausin da fararen idanunsa wad'anda suka nemi zautata, bai Ce komaiba ya janye ya maida kan Munubiya, “Sister naga drugs d'innan?”. yafad'a kamar anmasa dole. Ko kad'an Munubiya bataji maiya fad'aba, dan a saman la66ansa yayi maganar, tana shirin sake tambayarsa d'aya daga cikin dogaran ya maimaita mata a tsawace. Nikaina saida Na bud'e ido saboda tsawar, Na bankama dogarin harara ina magana k'asa-k'asa yan da babu mai jina, kajimin shegen dogari, dan tace batajiba zakawani daka mata tsawa?, shi mizaisa bazai bud'e baki yayi magana yanda kowa zaijiba? Mutum sai azabar Girman kai mtsoww, koma R bai iyaba. Duk maganar danake la66ana ne kawai ke motsawa, shikuma idon nasa nakan la66ana, dukda duba kwalin drugs dayakeyi, tsaf ya karanci duk maganar danakeyi. yayi wani munafukin guntun murmushi yana mik'ama Munubiya magungunan. Juyawa yayi yama Harun magana, sannan ya juyo ya kalleni yana fad'in “ALLAH yak'ara lafiya”. Harara Na zuba masa batare da tunanin zai ganiba, amma sai caraf muka had'a idanu. Janye idanunsa yayi a kaina yajuya yabar wajen yana cije lips d'insa da mamakin yarinyar nan da batada tsoro. su Safara'u Na zuba masa godiya, duk da zukatansu Na mamakin yanda yanuna tamkarma bai sanmu ba. Ko kallonsu baiyiba ya d'aga musu hannu, sukuma sunyine dama danya tanka musu. Harun ya tambayi Munubiya wane doctor ne ke dubani?. Ta Sanar masa. Addu'a yaymin sannan yabar wajen shima. Lumshe idanuna nayi zuciyata Na kaikawo, yanda Galadima yayi, saiya kuma tabbatar min da mafarki dai nayi kenan, bawai gaba da gaba ba yace muyi Auren Contract ba kenan. Innalillhi, mike shirin faruwa danine ni Hussaina, hawayen dasuke neman zubomin nai k'ok'arin had'iyewa, Munubiya kanta tashiga kogin mamakin yanda Galadima yay tamkar ma komai baita6a faruwaba, shin kodai shi baiga abinda yafaru a jaridar baneba?.... Batada mai bata amsa, su safara'u ma magana suketayi k'asa-k'asa a tsakaninsu, alokacinne kuma matan gidanmu suka shigo. Mamansu yaa hameed take tambayar wai wananan bashine Galadima ba na jikin jaridar nan?. “wlhy shine kuwa mama”. cewar Fiddausi. Haleematu ta kar6e da fad'in “mama kinga yanda ya nuna kuwa? tamkar ma bai gane su twins ba balle ya nuna yama San abinda yafaru a bayabaya tsakaninsu”. Murmushin mugunta mamansu ya hameed tayi, “yo ai dama saboda irin haka ake cewa Ku kare mutuncin kanku, danshi namiji komi yayi adone, sannan shi d'an manyan mutanene, ko kallonsa da abin babu mai sakeyi, amma Ku gashi har ana fasa aure, kamun kai dai dad'i gareshi ai dama, kum.......” Shigowar doctor tasaka maman su yaa hameed yin shiru, korarsu yayi gaba d'aya, yace subarni Na huta. Basuso hakanba, dan shirya cin zarafinmu maman yaa hameed tayi. Daganan gida suka wuce suna 'yan gulmace-gumacensu da dariyar mugunta. ★★★★★ Galadima kuwa yana gama zagaye-zagayensa a asibitin na duba marasa lafiya gida suka wuce. Bayanin doctor yabashi mamaki, wai wannan 'yar yarinyar keda hawan jini, itako miyayi zafi haka a rayuwarta”. wani sashi na zuciyarsa yabasa amsa da (6atancin da akai muku). Lips d'insa ya cije yana jan dogon tsaki, shikad'ai yasan burin daya d'auka akan dukkan Wanda yasamu da hannu a wannan lamarin. Sun biya birnin gayu plaza yaga komai yana tafiya dai-dai, daga nan suka koma masarauta. ★★★★ Nima a ranar da daddare aka sallamoni, nadawo gida nacigaba da shan Magani, yayinda biki keta gaba towa kuma. Har yanzu innarmu tana cikin damuwa dani kaina akan zancen aurena daba asan taka maimai angoba. Zancen galadima kuwa ai tini na shareshi, dan nabarsa amatsayin mafarki nayi, musamman kuma dana bincika banga number wayan daya baniba, a wayata kuma tun randa na tura masa massege na gogeta dama gudun kar wani yagani. Yanda 'yan gidanmu suketa rawar kai akan bikin saran 'yan uwanmu innarmu batayi, bazama ka ta6a d'auka itama zata aurar da 'ya'ya har biyu baneba. Mama Rabi'a ce ke tsaye akan komai, sai aunty salamah datazo da magunguna ta d'id'd'irka mana, mu bamusan namiye ba, takumace mudinga sha, saikuma had'ad'd'en sabulun wanka da mai data had'a mana, ga wasu turare masu sirrin k'amshi, takuma gargad'emu daga yanzu muna saka hijjab duk inda zamuje da nik'af, domin fatarmu tasami nutsuwa kar rana ta maidamu gidan jiya. Ni dai dagani har munubiya da to kawai muke binta, kuma duk abinda tace muyi munayinsa. Abbanmu yakira mama Rabi'a yabata wasu kud'i akan tak'ara amana siyayyar kayan kitchen da 'yan uwa keyi, tunda ita innarmu bawasu dangi ne da itaba dazasu tara mata. Sosai tamasa godiya, sanan tasanarma innarmu, ko babu komai taji dad'i, harma tamasa godiya itama. Tafiya mama Rabi'a tayi da k'ud'in, washe gari suka Shiga kasuwa itada inna lami, kaya masu k'yau suka sissiya mana dai-dai gwargwadon k'arfinmu. aka adanasu gidan inna lami duka. *_kwanci tashi_* Babu wahala wajen ubangiji, yau gashi abinda kowa yake jira yazo, domin kuwa ankawo lefen Haleematu, gaskiya angonta yayi k'ok'ari, akwati 5 abinta, kuma kaya masha ALLAH, sai-dai hakan bai hana 'yan gidanmu gulmaba, washe gari kuma aka kawo kayan Safara'u da Fiddausi. Suma dai kam saidai mak'iyi, amma jikin maman safara'u yayi sanyi, dan gaskiya kayan sauran duk sunfi nata. Itama dai akwati biyarne, amma kayan cikine basukai na sauranba. Again washe gari saiga na Fauziyya da Munubiya, mama Rabi'a tasan komai dake wakana a gidanmu, dan haka suka dage sukaima Munubiya lefe na 'Yar gata, wlhy ba fariyaba lefenta yafi na kowa, ranar har kukan dad'i nayi, domin banyi zaton hakanba. itama dai fauziyya angonta yayi k'ok'ari gaskiya. Tuni hassadar matan gidanmu tafito fili suka fara yada habaici wai an aro kaya anzo ana musu burga, da anyi aure sai ake maidawa d'ai-d'ai. Dagamu har innarmu babu Wanda ya tanka musu, dan munsan yau dai mune aciki sune a kwana🤣🥴. Rashin kawo nawa lefen kuwa ko a kwalar rigata bai dameniba, dan bama sanin mijin nayiba balle nadamu dawani lefen banza. saima Munubiya ce harda kukanta rurus akan wai saidai araba mana kayanta mu biyu. Nifa dariyama tabani wlhy. Ganin ni babu lefe yasaka su baba k'arami siyomin kaya masu k'yau na fitar biki har kala 10, aka d'inka min, sai takalma da bags da veils masu k'yau suma. Habaici dai kam munshashi wa su innaro da matan gidanmu, danma ita innaro gwaggo Safiyya na hanata ne, da bamu san tijarar dazata zubarba a ranar kam. A haka aka shiga satin biki, mu bamu wani gayyaci k'awayeba, daga Bilkisu sai su Ayusher, ashe Ayusher ta buga invitation na k'awaye suka raba itada Bilkisu bamu saniba. Abin mamaki ranar kamu sai ganin k'awayenmu mukayi harna secondary. munji dad'in hakan sosai kuwa. A ranar kamun saiga wasu mata hud'u sunzo wai dangin miji nane, su mama Rabi'a sukayi musu tarba ta mutunci, ba a nuna musu komaiba kuma, dukda a yanayin shigar talauci da sukazo, saidai zund'e da gulma irinta 'yan biki. Matan gidanmu kam komai ya kaimusu dai-dai, sai dariya da yada magana a kaikaice sukeyi. Da aka kaisu su gaisa da innaro taita musu yatsine-yatsine, harda tanbayarsu waisu garinsu ba'a lefene? dabasu kawoma jikartaba?. Basuce komaiba sai murmushi kawai da sukayi. Washe gari kuma akayi k'unshi, mudai namu aunty Salamah ce tamana, tana tsaye akan komai namu tamkar yayarmu ciki d'aya. A ranar kuma akaje a kaima sauran amaren jere, harda Munubiya, amma ni banda ni, tunda ba'asan ina za'aje ayiba. Aranarma Munubiya tayi kuka, nidai ina k'ok'arin danne zuciyata, saboda nabama innarmu kwarin gwuywa karta tada hankalinta. Aiko Alhmdllh ta dake tamkar komai baya damunta, tashige cikin abokan arzik'inta sunata harkoki. kowanne 6angare yacika da dangin matan gidanmu, abin tamkar fariya, namu 6angarenne kawai keda sauk'in jama'a, hakama gidan innaro yacika da danginta da dangin kakanmu. Tunda aunty Salamah tagama yimana k'unshi da gyaran kai dana jiki sai muka nufo hanyar gida, saboda yaa marwan yazo neman Munubiya harsau biyu, sai kiran wayarta yake yana masifa saboda tare yake da abokansa. hakan yasa muka taho gida. Gashi Yau zamuyi sister's and brother's day, duk da dai saima da yamma. ★★★★★ Galadima dake zaune a makeken falon Ummu hasheem, yanata bin jerin akwatinan da kallo, ga wasu daga 'yan uwansa zazzaune sunata kuma kimtsa kayan, aunty Mimi ta kalleshi, “kunga zanma mantafa, my k'ani ina kayan dana baka kayo gaba dasune?”. Yatsine fusaka yad'anyi yana gyara zamansa, “nifa nama manta inda suke, shiyyasa nace bazan d'akkoba ai”. Wata uwar harara ta watsa masa tace, “lallai bakada kai yaro, bar ganin matarka za'a kaimawa, suka 6ata biyana zakayi ehe” Murmushin gefen baki yasaki yana lumshe idanu, cikeda k'asaitarsa yace, “Samha! jeki bedroom d'ina ki duba, maybe suna can“. “bama kada tabbas kenan?” cewar mom. Bud'e idanunsa yayi yana murmushi, “no mom insha ALLAH sunama can. ni yanzu kam kun sallameni natashi natafi? dan zansa aje a d'auko su Akash a airport ”. Ummu Hasheem tace “kaje kawai, dama dan kaga kayanne, tunda kuma kace komai yayi ai shikenan”. Mik'ewa yayi yana fad'in “thanks you Ummu, nabarku lafiya”. Tunda yasamu yay escape sai ya sauke ajiyar zuciya, shi dariyama suke bashi dagasu har su papi, su Dan basu san auren shekara d'aya bane dabasu dinga wannan rawar k'afarba, sun wani zauna sun had'a uban kayan lefe, yad'an ta6e bakinsa kawai yana nufar sashensa. Komai na gidan sarauta mai tsarine, dan haka kai lefen MUNAYA da suke shirin yima a tsare akayisa, (papi ne yace Subari sai yau ana gobe d'aurin aure sai akai, tunda gidan su munaya basusan kosu su wayeba). An tsara iya wad'anda zasu kai lefenne. Bayan an gama zuba akwatunan a wata farar mota mai k'yau sabuwa dal aka rufe, driver ne kawai zai shiga cikin motar. Sai kuma motoci 6 da aka zaba wad'an da zasu kai lefen. Motar farko dogaraine, ta biyu kuma kuyangi ne, sai guda biyu 'yan cikin gidansu Galadima ne su hud'u, ko wacce mota mutum biyu, sauran biyun kuma 'yan 6angaren masarautar su Momma, suma su hud'u, kowacce mota biyu. sai Samha datasa kuka saitaje taga matar Uncle Sam. Aunty mimi harta korata da zare mata idanu saiga Galadima motocin na niyar tashi. Da kansa yabud'e mata gaban motar da aka saka akwatinan yace tashiga nan, idan taje ta gaida masa matarsa. Cikeda d'oki tace zataji Uncle Sam, bazaka bada komai akai mataba. Kansa yad'an dafe dan yakula Samha na neman k'uresa, shikuma yafad'a mata maganarne domin yanason agaban jama'a yadinga yana tsantsar k'aunar Munaya, a bad'ini kuma suna zaman aurensu na contract, shiyyasa ko lefennan baiji tsadar kud'in saba yabud'e bakin aljihu aka zuba kaya masu azabar k'yau, gakuma kud'in da Mai martaba yabada shima, dakuma sauran k'annen mahaifinsa. Hannu yasaka a aljihunsa yana duba kozai samu wani Abu, amma babu komai sai wata chocolates guda biyu, wadda ya d'akkota ne zaiba khaleel d'azun yama manta, mik'ama Samha yayi yace “gashi kibata”. Da dariya samha ta kar6a tace “Uncle ta gode to”. Kansa kawai ya jinjina mata ya shirin barin wajen. motocin suna fita daga masarautar saiya sauke ajiyar zuciya kawai. ★★★★ Gidanmu ya cakud'e da hayaniyar da akasan gidan kowanne biki da ita, bare mu daya kasance har auren mutum 6, dukda sai gobene d'aurin aure kuwa, yara sunata wasansu da tsalle-tsalle. A jere motocin suka shigo cikin anguwar, jama'a sai binsu da kallo sukeyi, dai-dai k'ofar gidanmu driver daya san gidan yay parking. Babu Wanda yay mamaki a 'yan kawo lefe, domin kuwa dama labari ya karad'e masarautar cewar Galadima'yar talakawa zai aura. Dogarawa da kuyangi suka fara fitowa, sannan suka bud'e motor da akwatina suka suka fara fitarwa. Nanfa jama'ar anguwa sukayi cirko-cirko suna kallon ikon ALLAH dan ganin akwatinan da aketa fitarwa daga mota. Batare da neman isoba Kuyangin suka fara kwasar akwatinan suna shiga dasu gidanmu..............✍🏼 😂😂😂 Team innaro kufito mu caskale yau🙊🤸🏻‍♀ ⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ Asha weekend lafiya😅✋🏻 *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu👏🏻😭_* * _*RASHIN SANI.......*_ *HAUWA A USMAN* _JIDDARH_ ```Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh``` 1⃣9⃣ Khulud ta kuma zaro idonta waje tace " kai my Sanah, cikin dariya Sanah tace " eh mana, " ni dai please kiyi man alk'awarin baki kuma ramawa please, tayi maganar cikin sanyinta, Sanah ta kuma yin dariya had'i da dafa kafad'ar Khulud tana kallanta ido cikin ido, cikin marairaicewa Khulud tace " please tana langwab'ar da kanta gefe, Sanah ta d'an k'ura mata ido kana ta sauke ajiyar zuciya had'i da cewa " nayi miki alk'awarin daga yau har abada duk abinda zai man ban kuma ramawa, cikin jin dad'i Khulud ta rungume ta tana cewa " yawwa my Sanah thank you so much, murmushi Sanah tayi kawai batare datace komai ba, ta rok'o hannun suka nufi part d'in kakannin su. Fitowa Hanash yayi zuwa harabar gidan, su Wajnah na biye dashi a baya, Papu yace " au kinga na manta Hanash zai fita batare dana aike shi bank d'in bako? Yayi maganar yana kallan Mimmee, tace " kaga kuma yau Friday ba, da idan ya aje su sai ya biya bank d'in, kafin su gama walimar shi yaje yayi abinda zayyi, Mimmee ta fad'a idanta kan Papu, " kuma daga yau ba bank har sai Monday, ga time na tafiya naga yanzu wajen 4:30pm, yayi maganar yana mikewa had'i da kallan agogon hannunsa, da sauri ya fita daga parlor'n yabi bayan su Hanash, Hanash na niyyar yiwa mota key, yaga Papu ya nufo su da sauri, a hankali Hanash ya fita ya nufi Papu, check Papu ya mik'ewa Hanash yana cewa " idan ka aje su a gidan walimar ka biya banki ka amshi wad'annan kud'in, sai ka saka su a account d'ina ko naka, Hanash yayi murmushi yana kallan Papu zayyi magana drivers biyu suka shigo gidan a lokaci d'aya, Papu yace " yauwa ga drivers nan sun dawo, bari na saka d'aya daga cikin su ya kai su gidan walimar, kai kuma sai ga je bank d'in, Papu yayi maganar yana nufar wajen drivers d'in, cikin taushi Papu ya fad'a musu, sannan ya sanar dasu Zohal su fito su shiga motar driver shi zai kai su, kana ya koma wajen Hanash dake tsaye inda ya barshi, Papu ya lura da yadda yanayin Hanash ya canja sosai, sannan walwalarsa da sakin fuskarsa ba kamar da ba, kallan Papu Hanash yayi kana yace " Papu wannan kallan fa? Ya fad'a yana dariya, shima Papun dariya yayi yana dafa kad'afar Hanash yace " bakomai kawai ina kallan d'ana ne, in kuma za'a hana ni ne to, yayi maganar cikin barkwanci, Hanash yayi dariya batare dayace komai ba, Papu yace " kaje maza ka dawo zamuyi magana da kai, Hanash yayi dariya kana yace " hala Papu ya manta yau Saturday? Papu ya zaro ido had'i da cewa " what! haba dai? Hanash yayi murmushi yace " Allah kuwa Papu yau Saturday, hala ka shafa'a ne? " Ka manta jiya mukaje sallar juma'a? Papu yace " na manta, kasan tsufa ya fara kamamu , abinka da tsoho, Hanash kuma yin dariya yace " kai Papu wanne irin tsufa kuma? "Bayan gaka nan kamar matashin sauryi kamar mu,, Hanash ya fad'a cikin tsokana, dayake sun saba wasa da dariya sosai da Papu, dan wani lokacin idan ka gansu sai ka rantse abokanai ne, Papu yace " kayya wanne matashin sauriya, muda samartaka ai sai dai a lahira a aljanna, jiya ai ba yau ba , tunda na haifi k'aton saurayi kamarka ai na tsufa, ko yanzu Alhamdulillah dan na mori k'uriciya ta, kai ma sai kayi k'ok'ari ka mori taka k'uruciyar, sanda nake kamar shekarunka na haifeka, amma kai gaka nan har yanzu 30yrs baka da ko budurwar, ko rowa kake man dan karna ga 'ya'yanka oho, inaga sai na mutu sannan zakayi aure ka haihu, Jadda dake jiyo su ta window ta, suka jiyo muryarta tana cewa " kyale ja'iri wallahi idan na gaji sai dai ya shigo gidan ya iske matarsa a b'angarensa, imma bak'in ciki kake man dan kar naga yaranka ehe, daga Papu har Hanash duk suka sanya dariya, Hanash ya shafa kansa yana kallan Jadda, Papu dake tsaye a wajen shiya hana shi ce mata komai, sai murmushi da yayi tayi shi kad'ai yana shafa kai, kallansa Papu yayi yana nazarin yanayinsa ya tabbatar akwai abinda yake damunsa, amma sai ya sabar yace " ka rik'e check d'in a hannunka, ranar Monday sai kayi kamar yadda na saka ka, "tom Papu ba damuwa Allah ya kai mu Monday, Papu ya amsa da " amin yana komawa part d'in Mimmee, iske ta yayi tana k'ok'arin shigewa bedroom d'inta, ganinsa yasa ta jiyowa tana kallan shi, yace " wai meke damunsa ne? Tace " wa? Yace " Hanash mana, naga kwana biyu yanayinsa duk ya canja, Mimmee tace " nima dai haka nagani kwana biyun nan, kamar yana cikin damuwa, Papu yace " kin tambaye shi ne? Tace " eh, "Ok meya ce maki? " Wai bai jin dad'in jikin sa ne, Papu yace " ok mu barshi zuwa nan da kwana biyu mu gani, Mimmee tace " Allah ya kai mu, muje ciki kayi wanka ko? Bayanta yabi yana cewa " kamar ko kinsan zafi nake ji, Hanash na komawa b'angarensa ya kuma zubewa kan sofa, had'i da runtse idannuwansa, shi har yanzu bai san so da soyayyar Khulud ke d'awainiya dashi ba, ta hana shi sakat, ta hana shi walwala da farin ciki, haka nan kullum yake jin damuwarsa na k'aruwa, babban burinsa a rayuwa yanzu bai wuce na sake ganinta ko sau d'aya ne a rayuwarsa ba. part d'in Ganez suka fara shiga suka iske Nisah zaune kusa dashi, Sanah tace " oh! ashe dai har yanzu ana tsinkar korawayen fure? Duk sukayi dariya kana Ganez yace " a'a aini idan bada ku zan tsinki korayan fure ba, ai a banza, Khulud tace " kinji shi zayyi mana wayo kullum yayi ta cewa idan ba mu ba sai rijiya, Sanah tace " kuma yana tsoran matarsa ba, Nisah tayi dariya kana tace " oh! kuji man yara, wato kun saka mana ido, ai irin haka ake so, Khulud tace " mijin ya rink'a jin tsoran matarsa? Nisah tace " eh mana, Sanah tace " ina fa dad'i miji ya zama mijin tace, an dai mayar mana da kakanmu tace kawai, Nisah tace " wannan ai kan tace ne ma, duk sukayi dariya kana suka fita suka nufi part d'in Danish, ganin Erum tayi kwalliya yasa su yin dariya, Khulud tace " wato ke har yanzu baki dai na kwalliyya bako? Erum tace " ina ni ina daina kwalliya, Sanah tace " kici zamaninki kici na wasu ko? "Sosai ma kuwa cewar Erum, " a'a kace yau amare nane a gidan, cewar Danish dake fitowa daga bedroom d'insa, Sanah tace " mune, munzo a bamu abinda akaci aka rage,, Danish yace " ku da kuke amare ina ku ina raguwa, ai sai dai sabuwar dahuwa, Khulud tace " ai dama kun saba yi mana wayo, bayan duk tsoron matan ku kukeji, Erum tace " ai irin wannan k'arshen ake so ayi yara, ku ma kuyi addu'ar Allah ya baku ita mu, Sanah tace " wai ma duk ba wannan ba, ina zaku na ganku duk kunyi kwalliya? " Mu da muke da walima yau har a tambaye mu inda zamu dan munyi kwalliya, Erum tayi maganar tana dariya, Khulud tace " a she walima ce daku, a ina kuma? Erum tace " sosai ma, kuma a nan gidan, Sanah tace " tab wai wacce walimar kuke nufi? Badai tamu ba ko? Tayi maganar a lokaci d'aya, Erum tace " walimar ku ko tamu? "Ai muke da walima kuwa, tunda mune manyan k'awaye, tayi maganar tana dariya, Khulud tace " mu dai bamu gayyace ku ba, kuma bamu san gayyar sod'i ehe, duk sukayi dariya kana suka fita, part d'in Juju sukayi, da sallama suka shiga, Didi ya amsa musu cikin fara'a, kana yace " 'yan candy ne yau a gidan namu? Sanah tace " mu ne, Didi ya kalli Juju yace " ina kika b'oye mana su ne? Juju tace " wacce ni? " Ai sai dai ka tambaye Mamun su, ni tunda sukayi candy ban sa su ido na ba, sai yau, ko irin kayan kayan candy nan ba'a kawo mana ba, balle muce mu shaida anyi candy, muce Allah ya sanya alkhairi, Khulud tace " kai Juju Allah bamu zauna bane, mu ta yawan zuwa saloon da k'unshi, Sanah tayi dariya kana tace " Juju ku da zaku bawa wasu ma, kayan candy kuma ga walima nan kun shirya ku da kanku, sai ku shaida anyi candy kuyi addu'ar Allah ya sanya alk'airi, Didi yayi dariya yace " wai Sanah baki abin magana, ke dai ba'a tab'a k'ure ki ta wajen magana, Juju tayi dariya tace " ai ni nayi shiru tunda an fini baki,,, dama hausawa sunce dokin mai baki yafi gudu, Didi ya kuma yin murmushi kana yace " Sanah yaushe jamb d'inku zata fito? Sanah tace " naji ance this coming Monday, Juju tace " wacce university kika cike? "First choice BUK second kuma ABU Zaria, Didi yace " masha Allah Ubangiji ya taimaka, Allah ya bada sa'a, duk suka amsa da Amin, har Khulud dabata zana jamb d'inba, dan cewa tayi ita ta gama karatun boko har abada, Juju ta kalli Khulud kana ta mayar da kallan ta ga Didi tace " 'yar Abbu da Mamu ita aure take so, Khulud ta d'ago kanta da sauri suka had'a ido Juju tayi saurin sadda kanta k'asa tace " Allah Juju ba haka bane, tayi maganar a shagwab'e, Juju tace " idan ba haka bane to yaya ne? Khulud tace " Allah ni ban san cigaba da karatun ne kawai, ni kwata-kwata ban tab'a sha'awar yin karatun boko mai zurfi ba, Juju zata kuma yin magana, Didi yayi saurin cewa " haka ne ai kowanne mutum yana da nashi ra'ayin, hakan ma da kikayi dai-dai ne dabaki yaudare iyayenki kin shiga jami'ar ba, kana kik'i yin karatun ko wata matsala ta faru, so ni ina ganin kinyiwa kanki da Abbunki adalci, Allah ya zab'a maku abinda yafi alkhairi a rayuwarku, ya haskaka rayuwarku ya sanya albarka acikinta, duk suka amsa da Amin, fita sukayi suka nufi wajen da aka tanada dan yin walimar da tuni k'awayensu sun fara zuwa, sosai walima ta kankama haik'an, aka ci aka sha sosai dan sosai Abbu ya saki bakin aljihunsa dan nuna tsantsar farin cikinsa na kammala karatun yaransa lafiya, sosai aka rarraba kyaututtuka, kana kowa ya watse cikin farin ciki aka gama walimar lafiya. Sannu a hankali matsanannaciyar soyayyar Khulud tayi mugun kama Hanash, ta addabi ruhi da gangar jikinsa, kwata-kwata ya rasa sukuni da walwalarsa, ya rame sosai dan raban dayaci ishashshen abinci ko ya samun bacci har ya manta, kullum yana cikin bedroom ko parlor'nsa, dan ko fituwa sosai ya dainayi sai dai ya fito ya gaida iyayshi ya koma, yauma kamar kullum kwance yake a d'akinsa ya tsunduma duniyar tunaninta, idanshi rufe babu abinda yake gani sai ita tsaye a gabansa, tana sakar mishi k'ayataccen murmushinta, jin knocking yasa shi bud'e shu'uman idanuwansa, k'ofar ya zubawa ido na tsayin lokaci, batare da yayi wani yunk'uri ba, sake knocking akayi a karo na biyu, dakyar ya iya cewa " waye? Muryar Papu yaji yace " mu ne, dan sun kasa jurewa ganinsa cikin wannan mawuyacin yanayin, da sauri ya mik'e ya bud'e musu k'ofar suka shigo, akan sofa duk suka zauna, a hankali Mimmee ta d'ora hannunta akan kafad'arsa, had'i da zubawa d'an nata ido, Papu ma ya zauna kusa dashi ya zuba masa ido, kansa ya duk'ar dan ya san kwanan zancen, muddin akace bashi da lafiya ko yana cikin damuwa to gaba d'aya gidan babu mai yin walwala, a hankali Papu ma ya d'ora hannunsa akansa kana ya kira sunansa, " Hanash, "na'am, Hanash ya amsa cikin ladabi, " meke damunka? Cewar Papu a tak'aice, murmushin k'arfin hali Hanash yayi kana yace " babu abinda ke damuna Papu, yayi maganar while kanshi k'asa, Mimmee ta shafa kansa kana tace " Hanash please karka b'oye mana abinda yake damunka, ka daure ka sanar damu koda babu wani abu da zamu iya yi akai, sai mu tayaka da addu'a, ta fad'a cikin damuwa, murmushi Hanash ya kuma yi kana yace " ba ni da lafiya ne, Mimmee zazzab'i da ciwon kai ke damuna, ido Mimmee ta zuba mishi tana nazarinsa dan ita kwata-kwata bata yarda da abinda yace ba, Papu yace " kaje hospital? Hanash yace " eh Papu, "me sukace yana damunka? Papu ya kuma tambayarsa, d'an shiru Hanash yayi kafin yace " Malaria, " to ikon Allah kai ko ina kaga sauron daya cije ka? Mimmee ta fad'a tana kallan kwayar idansa, murmushi yayi kana yace " Mimmee, cikin shagwab'a, Papu yace " shi ciwo ai daga Allah ne, ba ta inda baya shiga jikin mutum ko son? Yayi maganar cikin tsokana, dan shima yadai ji Hanash ne kawai, amma bai yarda da abinda ya fad'a ba, babu yadda Papu da Mimmee basu yi akan Hanash ya sanar da su damuwarshi ba, amma yak'i yace babu abinda yake damunsa, Papu yace " Allah ya sauwak'e, ya amsa da " Amin, kana suka fita, suna fita Hanash ya koma ya kwanta, had'i da rufe idansa. Ranar Monday jamb ta fito, Sanah cikin murna da d'oki suka je ita da Aarib & Khulud suka duba, a cafe, aiko taci sosai dan ta samu 251, tsalle ta buga ta rumgume Khulud da Aarib cikin matsananciyar murna, motar su nayin parking a harabar gidan ta fito, ta shiga kwalawa Halan kira, da gudu ta shiga part d'in Halan, ta iske ta parlor zaune ita da Ziyad, cikin murna ta fad'a kanta, ta ma manta da tsohon cikin dake jikin Halan, Ziyad ya daka mata tsawa had'i da cewa " ke baki da hankali ne ko baki ganin abinda ke jikinta? Bata kula da tsawar daya daka mata ba, sai ma kiss datayi mishi a kumatu, cikin murna tace " Yaya naci jamb, ta fad'a tana tsalle, dariya Halan tayi tace " kai masha Allah gaskiya nima nayi murna, badan kayan dake gaba na ba, da har dani za'ayi tsallan, Ziyad yayi dariya yace " bani abu na inyaso sai kije kiyi tsallanki, Halan ta kalleshi had'i da zumb'uro baki tace " Allah da ana bayarwa ai bama sai ka tambaya ba, Sanah da Khulud suka fita da gudu suka nufi part d'in Mamu, suna zuwa Sanah ta fad'a kan Abbu, yace " kai Sanah ke dai baki girma, naga alamar so kike ki karya ni tunda baki ganin na tsufa yanzu, Sanah tayi mishi kiss tace " Abbu albishirinka, yana dariya yace " goro, tace " fari ko ja? Yace " fari tass, tace " Abbu na ci jamb, Abbu yace " wai dole ayi murna, Mamu tace " masha Allah, saura waec & neco, Abbu yace " suma duka za'a cinye su, in sha Allah, fita sukayi suka nufi part d'in Juju, nan ma aka sanar mata anci jamb, murna kam ba'a magana, a week d'in waec ta fito, Sanah ta samu result mai kyau, result d'inta yayi mugun kyau, bayan two weeks BUK ta kira su first UME, bayan week nan ma result ya fito, ta samu taci, suka bata Admission letter na BSC COMPUTER SCIENCE. Kullum Hanash bashi da wani aiki sai mafarkin Khulud, da tunaninta ko idansa ya rufe ita yake gani, koyaya ya rufe idansa ita yake ya gani, abun duniya duk ya dame shi, ba shi da wani burin daya ce na sake ganinta a yanzu, ko da sau d'aya ne a rayuwarsa. Yau itace rana ta farko da Sanah zata fara hallartar BUK, ta gama shirinta tsaf cikin riga da siket na material red color d'inkin yayi masifar yi mata kyau, ya amshi jikinta sosai, ta saka high hill shoe ta yafa mayafinta mai kyau kalar flowers dake jikin material d'in black, sosai Sanah tayi shegen kyau, duk da ba wani make up tayi ba, ta dayyi simple make up abinta, wanda ya bayyanar da tsantsar kyauta, har cikin makarantar Aarib ya kaita, sai da yayi mata fad'a sosai kana ya tafi, sannu a hankali take tafiya harta isa department d'insu, tambaya tayi, aka nuna mata, inda zasuyi lectures yau, dayake tana da time table na duka courses & time d'in su, a hannunta tasan Computer lectures zata fara attending, zama tayi a inda taga students na zama, zamanta ke da wuya ta fara jiyo hirar students, " yau fa Sir Aryan ne damu, kasan ko ba sauk'i, d'ayan yace " wallahi ko ni gaba na ma sai fad'uwa yake yi, tun jiya dana duba naga shine damu hankali na yake a mugun tashe, wani daga gefe yace " kai ai Malamin nan bai da kyau, d'ayan yace " kaga fito sak a mutum kai tsaye kace bai da mutunci, d'ayan yace " ni fa yana mugun ban mamaki shi ko irin na sauran lectures d'in nan bayyi, d'aya yace " me? " San mata mana, d'ayan yace " kai tanan wajen ai Sir Aryan yayi wallahi, ba ruwanshi da mata, duk kyanki yanzu zai yarfa ki, ba kamar sauran lectures d'in ba, shegu da sunga mata sai suyi ta rawar jiki, idan mune 'yan uwansu maza tsakanimu dasu ba mutunci, sai su rufe ido su karta mana, amma shi kwata-kwata mace bata isheshi kallo ba, naga 'yan mata dayawa sunyi mugun matuwa akansa, d'ayan yace " aiya had'u ne ga kyau ga kud'i, kaga kuwa ai dole mata su matu, tunda ready mate ne, d'ayan yayi dariya yace " aiko suna shan dizgi da wulak'anci a wajensa ba, dan yanzu zai kartawa mutum rashin m, idan ta kama ma ya yarfa maka mari ba ruwanshi, shege ga girman kai da d'agawa da jan aji dan sai kayi mishi magana goma amma dakyar idan yaga dama zai amsa maka d'aya , d'ayan yace " kai ai ya iya d'aukar wanka dacin uwar sutura, yana zagin gizna ta asalimma, ni na rasa uban me yake yi a makarantar wallahi, "hmmmm ga babu ruwanshi da ke wai mace ce, shi hukunci d'aya yake yi tsakanin mace da namiji, idan ya riga ka shiga class ko waye ubanka kuma ko uban ya tsaya maka ya d'aure maka gindi baka shiga, d'ayan ya duba agogo yace " sauran just 5 minutes ya shiga fa, kusan kuma baya African time, d'an tsaki Sanah tayi a hankali kana ta mik'e tabar gurin, saboda duk gurin wajen mutum 100, maganar mutum d'aya suke tayi Sir Aryan, duk inda students sukayi d'an group, maganar shi kawai sukeyi mata da maza, daga maganar had'uwarsa kyansa, gayu, ajinsa, sai ta wulak'anci da dizginsa da kuma girman kansa, da yadda mata suka mato akansa yake wulak'antasu, shiyasa duk randa yake da lectures dasu suke kaffa-kaffa. Can gefe ta koma ita kad'ai ta zauna, ita kad'ai kasancewar yaune farkon zuwanta bata san kowa ba, tana daga zaune taga wata matsiyaciyar had'add'iyar mota ta danno kai cikin makarantar, students na ganin motar suka kai duba zuwa number motar dan su tabbatar idan shi, saboda baya hawa motar d'aya, duk nacinka baka isa kace ga yawan motocinsa ba, ta number motarsa kad'ai suke gane shi ne, saboda sunan family d'in su ne a duka number motacinsa,, ai students na tabbatarwa shine, suka fara gudu maza da mata ana rige-rigen shiga class. Yana yin parking, ya zare key d'in tare da komawa ya kishink'id'a jikin kujerar, ido ya lumshe tare da fesar da numfashi mai sanyi, a hankali ya kuma bud'e idon tare da sauk'e ajiyan zuciya, yana mai shak'ar k'amshin jikinsa dana mortar, a hankali ya sa hannun damanshi ya dafe saitin k'ahon zuciyarshi dan jin gabansa yana muguwar fad'uwa da k'arfi, bugun zuciyarsa ya k'aru sosai, zuciyarsa ta rink'a bugawa so past, idansa ya kuma lumshe yana k'ara d'an kishingid'a akan kujerar motar, a hankali ya furta " innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, saboda yadda yake jin duk ilahirin jikinsa ya mutu, gabansa na mugun fad'uwa zuciyarsa na bugawa da tsananin k'arfi, addu'ar yayi ta maimaitawa dan baya son ayi mishi African time shiyasa shima baya son yayiwa d'alibanshi, bere daga inda yayi parking yana iya hango yadda suke sassarfan shiga class, sharshesa ya fitar tare da d'an laso lips nashi, hadi da d'an cizawa dan kauda kasalar dake saukar mai a jiki, a hankali ya b'alle marfin motar tare da zuro k'afarshi d'aya woje, baki ya d'an tab'e ganin yadda wasu matasa suka wuceshi da sassarfa, gudun karya rigasu shiga class, ya hanasu shiga, fitowa daga cikin motar tare da jawo laptop nashi, ya bud'eta tare da dorata kan hannunshi daya mik'ar, yana kuma d'an lallatsashi cikin k'orewa, ajiyan zuciya ya sauk'e tare da fara takawa zuwa class d'in yana mai jin dad'in iskar dake busawa sirrai da fawowi suna shawagi tsuntsaye na kai komo ga k'amshin furanni dake ratsashi. Cikin takunsa na isassun maza masu haiba da kamala ga tarin nagarta yake tafiya cap-cap sautin takalminshi ke ratsa wurin in dalibai sun hangoshi sai suna rusunawa tare da ratse mishi. Ganin yadda students ke gudu yasa Sanah kai idanta kan motar dataga kamar an saka MOLI'S 15, amma data duba so sai taga kamar ba haka bane, baki tad'an tab'e kana ta mik'e cikin takunta mai daukar hankali tabi bayanshi, ta nufi class itama, daga bayansa ya rink'a jin kamar takun mutum a bayansa k'at-k'at, Fuska ya kuma had'ewa dan ya gane mace ce, daga k'asa ya kalli k'afarta data sha kunshi mai ja da bak'in lalle yayi masifar yi mata kyau, gabansa ne yayi muguwar fad'uwa lokacin daya d'ora idansa akan k'afarta, sake had'e rai yayi , kana ya cigaba da tafiya, yana tafiya tana binsa a baya, har suka zo gaf da isa class d'in, Kai ya d'an jinjina tabbatarwa da yayi class d'in sa zata shiga , hankalin shi na kan laptop d'inshi, hannunshi mai yin typing d'in ya d'an d'aga shi saman kafadarshi ta yadda zata gani, sanan ya had'e doguwar yatsarsa ta tsakiya da babbar yatsarsa ya kettasu sau d'aya ta yadda ya bada sauti, sannan ya had'e yatsunsa biyu ya kad'asu kamar mai buga fiyano ya mata nuni data tsaya inda take karta biyoshi, batare daya juyo ya kalle ta ba bai kuma tsayaba yaci gaba da takunshi zuwa cikin class, Itako Sanah bata gane abinda yake nufi ba, dan haka taci gaba da binsa a baya, Kai ya jinjina tare da yin gutun murmushi, mai dauke da alamar zaki gane kurenki, kana ya cigaba da tafiya har suka k'arasa cikin class d'in, Sanah tazo zata wuce mazaunin d'aliban, *"Keeh"* kamar daga sama sautin muryarsa ya ratsa shirun daya ratsa ajin,sai sautin takalminta dake amsakuwa, shirune ya sake ratsa ajin duk sunsha jinin jikin su, ita kuwa Sanah kai ta d'ago ta kalleshi ,Amman bata ga fuskarsa ba dan baya ya bata, sai gashin k'eyarsa da ta tsurawa ido ganin shi a kwance lub sai wani lauyewa a yayi ya bi k'eyan nashi yana Shek'i, tana cikin nazarin da me tayi mishi ta kuma jiyo muryarshi na ratsa ajin baki d'aya taji tajiyo muryarsa nacewa yana cewa, *"kneeling down,"* ya fad'a still bai jiyo ya kalle ta ba, juyawa tayi bayanta taga babu kowa sai ita kad'ai, cikin mamaki ta kalli bayansa dan ita a iya saninta tasan ba'a saka Patick a jami'a. Cikin mamaki ta kuma kallan bayansa, batare daya jiyo ba taji yace *"ko bazaki kiyi bane?"* Muryar dataji ta daki dodon kunnenta, tasa gabanta mugun fad'uwa a razane ta kuma kallan bayansa, babu damar taga fuskarsa saboda ya juya mata baya, a hankali Sanah ta d'an zumb'uri baki kana tayi kneeling down d'in, gaba d'aya students mamaki ya gama cika su, duk da sun san halinsa, sun tabbatar zai iyin abinda ma yafi hakan, dan sun san mari ko dizgi abu ne mai matuk'ar sauk'i a wajensa, amma basu tab'a ganin yasa wata ko wani kneeling down ba, sai yau kuma daganinta new comer ce, students suka rink'a yin dogon wuya suna l'eka ta, jin muryarsa ta fara explanations yasa duk suka shiga hankalinsu. Sanah na nan har ya gama lecture tana ta zumb'ure-zumb'uren baki, Cikin k'asaita ya fito zai tafi , ganin ya wuce ta gabanta amma bashi da niyyar ce mata komai, yasa ta cewa *"Sir to ni wuni zanyi a nan ne? "* Tsayawa yayi cak a inda yake, kana ya juyo da fuskarsa a hankali ya zuba mata ido, had'i da hard'e hannayensa a k'irji, mik'ewa Sanah tayi batare daya bata umarnin tashi daga kneeling d'in ba, kanta durk'ushe tana kakkab'e siket d'inta, tana yin magana k'asa-k'asa, "eh wato kai zaka fece gidanku ni kuwa in zauna a nan, sai kace baiwar gidan ku ko, hegen k'eya! da nad'edd'en gashi." dan ita a tunaninta ya tafi shiyasa ta d'anyi halin, baki ta murgud'a tare da mik'ewa tsaye, d'ago kan da zatayi, keda wuya sexy eyes d'inta, suka sark'e cikin na *SIR MOLI* dayake tsaye hard'e da hannuwa yana kallan ta.................. _Aunty AISHA ALIYU GARKUWA_ _kina tambayar inda nakai miki Sir Molinki to gashi nan na maido miki abinki_ ~To fans masu tambayar ina nakai Sir Moli na b'oye har tsayin six years, gashi nan ya dawo~ ~sai a cigaba da gashi a d'ora daga inda aka tsaya~ *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻1⃣9⃣ .......Kallone ya koma sama yayinda kuyangin suka shigo cikin gidanmu, na d'akima tuni sun fara rige-rigen fitowa, baba k'arami da fitowarsa kenan daga sashensa yak'araso ga kuyangin, domin tambayarsu daga ina haka?. Baiwa d'ayace tabashi amsa da fad'in basu kad'ai bane, masuyin bayanin suna waje. Fita yayi sukuma suka ajiye kayan gefe suka kuma fitowa domin kwaso sauran. Muna falo a zaune inna lami ta tsaremu sai mun sha romon wani nama da aka dafa k'anana, sai yatsine fuska mukeyi saboda rashin dad'in naman. shigowar Ahmad da Aryaan da gudu yasa mama Rabi'a tambayarsu lafiya?. Ahmad yace “mama wlhy bak'ine da akwatina da yawa suka shigo”. Gaba d'aya muka zuba masa idanu, kafin wani yay masa tambaya a cikinmu mukajiyo sallamar baba k'arami. Innarmu ce tamik'e domin fitowa, ganinsa da manyan mutane cikin alk'yabbu yasata fad'in “baba k'arami bak'i mukayi?”. Cikin washe baki yace, “wlhy kuwa maman biyu ”. Itama murmushine shinfid'e a face nata, tabasu hanya suka shigo falon, duk suka zazzauna. Muduka muka durk'usa muka gaisasu, yayinda suka kuma gaisa dasu innarmu cikin mutunci. Fita baba k'arami yayi yasa yaa Anas ya kunna Gen..... dayake babu nepa. Shikuma yakuma fita da hanzari domin nemawa wad'annan bak'i masu bazata kayan tarba, bayan yakira Dady da Abba ya Sanar musu. Kaf matan gidanmu suka shigo, kowa yanason jin daga ina kuma. Mukam d'akinmu muka koma muda su Ayusher muna hasashen bak'i daga ina haka? da gani dai kasan jinin sarautane, ko kad'an ban kawo Galadima a rainaba ma, dan narigada Na shafe labarinsa ni. Suna cikin gaggaisawa da matan gidanmu saiga innaro tashigo, kai kace an wurgotane. baki tarik'e tana fad'in “o ni Marwanatu, manyan bak'i irin wad'annan surasa gurin sauka sai 6angaren Ai'sha? kuko bayin ALLAH daga ina haka? ”. Su aunty Mimi basu fahimci zancen taba, dan haka duk sai sukayi d'an murmushi, matan gidanmu kuwa kowacce tayi k'asa da kai dariyar mugunta Na cinta, Innarmu dai bata tankaba, hakama mama Rabi'a, sai inna lami ce tace, “yo inna in banda abinki waka hana rana fita idan lokacin fitar tata yayi?”. Kallonta innaro tayi zatayi magana baba k'arami yashigo da sallama, su Yaa Anas na biye dashi da kayan ciye-ciye nik'i-nik'i, bayan sun ajiye suka gaishesu cikeda girmamawa suka fita. Zama baba k'arami yayi suka sake gaisawa, sannan yace, “kufayi hak'uri, mukam duk kun sakamu a duhu wlhy”. K'asaitaccen murmushi aunty Mimi tayi, domin dama papi yamata bayani akan komai na 6oye musu dasukayi. ta gyara zamanta sosai “Alhaji daga masarauta muke, munkuma zo kawo kayan k'anwatane Gimbiya munaya”. Kusan kowa dake falon saida ya waro idanu waje, domin jin furicin aunty Mimi, wasuma zuciyar tasu kad'an tarage tayo tsalle waje. Aunty Mimi bata damu da yanayin nasuba tacigaba da fad'in “kuyi hak'uri fa, nasan nakuma sanyaku a wani duhun, mai martaba sarki Abdul'fatah da maimartaba sarki Jalaludden Abubakar, sune sukazo Neman auren yarinyar Ku Munaya wa d'ansu Galadima Muhammad Sameer Saifuddeen Abubakar, sun 6oye muku kansune saboda wani dalili, amma sun aikomu da sak'on ban hak'uri a gareku, yanzu dai mun kawo kayan lefen Munaya ne gasunan”. Jin jina kai kawai baba k'arami ke iyayi, bakinsa yakasa rufuwa saboda d'unbin farinciki da al'ajabin dake dank'are a zuciyarsa, yanzu nan daman manyan sarakunane agabansu a wancan karon sukazo Neman auren d'iyansu, lallai sun godema ALLAH dabasu aikata wani Abu Mara k'yauba agaresu, lallai ya yarda kwarjinin mulkine yasakasu mik'a Auren d'iyarsu ga mutanen dabasu saniba. Ai su madam innaro sai aka zauna k'asa babu nauyi, muryarta har zuga take tace “ranki ya dad'e wai gaskene saboda ALLAH?, kokuwa wasa kikeyi?”. Murmushi aunty Mimi tayi, sannan ta kalli su Ummu hasheem da suma suketa murmushi, kallonta ta maido akan innaro, “hajiya kaka mizaisa muzo muyi muku wasa irin wannan akan magana mai muhimmanci irin ta aure, tabbas maganar nan gaskiyace, munama fata gobe idan ALLAH ya kaimu iyanzu Munaya tazama d'aya daga cikin zuri'ar masarautar gagara badau”. Innarmu da mama Rabi'a juna suka rungume suka fashe da kuka, yayinda innaro tamik'e ta callara gud'ar data jawo hankalin tawagar jama'ar 'yan biki, sai kawai tashiga taka rawa. Dariya sosai tamaba su aunty Mimi, shi Kansa baba k'arami dariyar yayi yana girgiza Kansa da mamakin innar tasu mai kayan arzik'i Dana tsiya. Matan gidanmu kam ba'a magana, kowacce tayi d'if takasa koda kwakwkwaran motsi, kowaccensu jitake tamkarma tafasa ihu take a nan. Muryar gwaggon halimatu na rawa tace “wai da gasken dai Munayar gidan sarauta zatayi aure?”. “kwarai kuwa”. ‘innaro tafad'a tana mata wani kallo, “jikata sai gidan sarauta, masu bak'in cikin kuma sai a mace”. Lallai maganar innaro tadaki zukatan dukkan matan gidanmu, Sanin halin innaro da baba k'arami yayi saiyace duk afita abama bak'i waje susha koda ruwane. Jiki babu kwari sukaita Jan k'afa suna fita Su da danginsu 'yan biki da gud'ar innaro tajawosu shigowa. bak'in cikin kuwa k'arara a fuskokin wasunsu, maman su yaa hameed tayi taga-taga zata fad'i saida aka taryota. Gwaggo Safiyya tace “lallai jama'ar gidannan yau ake *RAINA KAMA KAGA GAYYAFA* duk Wanda kake Kallon bai kaiba to tabbas watan watarana shine zai kereka, babu ruwan arzik'i da mugun gashi, Wanda yace shine to tabbas bashi baneba”. Su Ayusher suka shigo suna gumtsa mana, kallonsu kawai nakeyi amma badan na gaskataba, munubiya ta rungumeni ta fashe da kukan dad'i, kallonta kawai nakeyi nakasa koda motsi, to murnar Auren shekara d'aya zanyi? Kokuwa murnar Ashe galadimane mijin nawa? bawani can da ban ba kamar yanda muketa hasashe?. Ban iya ta6uka komaiba wata k'yak'yk'yawar budurwa tashigo, daka ganta kaga wadda Hutu yagama ratsawa, babu shakka zamu iya zama sa'anin juna da ita, fuskarta d'auke da murmushi tace, “to ina amaryar Uncle Sam d'in?”. Feena ta nuna ni da hannu itama tana murmushi. Gadon ta hayo batareda jiran abata iziniba, ta mik'amin Chocolates guda biyu tana kuma fad'ad'a murmushin nata. Cikin mamaki muryata a sanyaye na girgiza mata kai nace “yar uwa namiye?”. Hannuna takamo tasakamin tana 'yar dariya, “inji Uncle Sam yace nabama matarsa, sunana Samha, d'iyar yayar Uncle Sam ”. Duk da mamakin daya cika zuciyata, hakan bai hani mata murmushiba, nace “nagode Samha”. Tad'an langa6e kai alamar itad'in shagwa66iyace tace , “zan dai fad'ama Uncle Sam kin gode, lallai Uncle ya iya za6en k'yak'yk'yawar sarauniyar gagara badau mai jiran gado insha ALLAHU”. dariya su Bilkisu sukayi, nidai nakasa cewa komai, sai d'an murmushi danayi. Ta dafa munubiya takuma fad'in inason twins sisters arayuwata, dan ALLAH nima kuna sona?”. Yanzun kam kasa daurewa nayi, nima saida na dara kamar yanda su munubiya ke dariyar, nakula ko kad'an Samha batada girman kai irinna 'ya'yan sarauta, sannan tanada surutu gaskiya”. Cikin shagwa6a ta langa6e kai gefe, “ALLAH da gaske nake kubarmin dariya, ina addu'ar ALLAH yasa nanda wata 9 aunty ki Haifa mana twins muma”. Amin su Ayusher suka amsa atare. Matsowa tayi kusa dani tafara mana hotuna, nidai nakasa ma magana, lallai Samha akwai rawar kai, ta tubure da shagwa6a wai sainayi murmushi kamar yanda munubiya tayi, tanason taje tabama Galadima tagani kozai iya banbancemu. Babu yanda na iya dole na murmusa akayi, sannan mukayi gaba d'aya. Bata bar d'akinba saida mama Rabi'a tashigo kiranta zasu tafi, aikam kamar tayi kuka, dan bataso tafiyarba, sai dai tace anjima zasuzo wajen brothers and sister's event. Har k'ofar gida su Ayusher suka mata rakkiya, dan lokacin su aunty Mimi harsun fita, sunso ganina amma sukayi shiru kar aga kamar dawata manufa sukayi hakan, sun hak'ura tunda dai insha ALLAH gobe ina cikinsu. Basuci komaiba dai a kayan da'aka jibge musu sai ruwa, dan haka baba k'arami yasaka aka bisu dashi mota, yace inhar ba wai bazasu iya cin cimar tamu bane to dan ALLAH suje dashi koda bazasuci ba su bada. Godiya sukayi, suna mai yaba halaccin wannan gida mai cikeda karamci, dukda dai sunkula akwai lauje cikin nad'i gameda wannan family d'in, musamman yanda wasu suka kasa 6oye hassadarsu, aunty Mimi ta murmusa a zuciyarta tana fad'in Ashe ba masarautar mu kawai baceba keda irin wannan kitimurmurar ta family. Mukulin farar motar da aka zubo akwatinan suka dank'ama baba k'arami sukace ta amaryace. ai yanzu kam rasa abin fad'a baba k'arami yayi, yak'agara 'yan uwansa su dawo suga wad'annan tarin baiwa da hikimar ubangiji da yayma d'iyarsu, wadda akulum ake ganin mahaifiyar yaran a k'ask'ance acikin gidan, sai gashi tazama *RAINA KAMA.....* Bak'i na tafiya gwaggo Safiyya tasaka aka baje manyan tabarmi a tsakar gida, aka fiddo akwatinan domin kowa yagani, makwafta duk sun shigo suma kam dan kar ayi babusu. Gaba d'aya gidan yacike da shewa da hayaniya, tun anama irga kayan har aka bari, saibi da idanu, 'yan bak'in ciki kam sun kume waje guda, sai kukan zuci, wasuma kasa daurewa sukayi suka bar wajen. Kasancewar su Ayusher duk suna can nashige toilet d'inmu nashiga raira kuka, nifa bammasan yanda zan fasalta muku yanda nakejiba wlhy. ★★★★ A 6angaren sister's d'ina kam su Safara'u harda kukansu, fauziyya ce kawai ta nuna farincikinta, dan har d'aki tashigo ta rungumeni tana ALLAH ya sanya alkairi. maganar tashin hankali ga jama'ar gidanmu ba'a magana, sunma rasa yanda zasu masalta lamarinma, maman yaa hameed data kasa hak'uri saita saka masifa da zage-zage wai ai munafurcine su abbanmu suka shirya, wannan zancen k'aryane akwai magana a k'asa, 'yan koranta ma irinsu momy Hadiza suna tayata. Nanfa gidan ya hargitse da hayaniya, kowa da abinda yake tofawa, innaro dai Abu biyune ya dameta, farinciki dakuma damuwar abinda tayita ma innarmu shekara da shekaru, yau kuma gashi ALLAH ya d'aga darajarta, ita dawanne ido kuma zata kalli Ai'sha. Babu Wanda ya tanka a 6angaren innarmu, saima farinciki dasu mama Rabi'a ketayi abinsu, inna lami kuwa da aunty salamah sunata callara gud'a dawasu acikin matan anguwarmu, hakanne yakuma harzuk'a su maman Safada'u, suka murje idanu sunata zuba tsiya, danginsu na tayasu. Innarmu dai tana daga cikin d'aki abinta, sai zuba murmushi take tana sharar hawayen dad'i, yau kokad'an rashin mutuncin 'yan gidanmu bai 6ata rantaba, saima wani farin ciki dasuke sakata. 🤣🤣 Maganar sisters and brothers event kam ai bai yuwuba yau, dan gidanmu gaba d'aya a harmutse yake, ga 'yan anguwa sunata turuwar zuwa ganin kaya harda mota. Nikam ma zazza6ine yagama rufeni tunda nagama kukan, duk wannan kacaniya da akeyi ina cikin bargo k'udundune, su munubiya kam sunacan tsakar gida sun kasa sun tsare akan kayan gudun masu suruf bahana😜🤣. Da k'yar aka tartare kayan aka kaisu falon baba k'arami kasancewar magriba ta gabato, sai bayan isha'i su Abba da Dady suka gani, ranar Abbanmu shima saida yayi kukan dad'i, ALLAH Sarki Ai'sha, nagodema ALLAH da wannan babban al'amari yashigomin ta 6angaren tsatsonki, kema yanzu k'ya samu 'yancin kanki agidan mijinki, 'ya'yanki zasu samu 'yanci a gidan mahaifinsu, dama akance ka yarda da k'addara kakuma godema ALLAH a yayin da ya jarabceka, Ashe sharrin da akama d'iyarsa zai zame mata alkairine, sun had'ata da babban mutum domin 6atanci agareta dashi kansa Ashe zai zama sanadin alkairi a rayuwar yaranne, dan yasan inba dan wannan abin yafaruba ina Galadima zai ga munaya har iyayensa sunema masa aurrenta? hikimar ubangiji yawane da ita, yakan jarabeka domin kankare zunibinka, kokuma danya d'aga darajarka ta inda bakayi zato ko tsammaniba. ★★★★★★ Labarin tarbar mutunci dasuka samu tuni ya karad'e masarautar, wasu kam dariyama abin yabasu, ina wata tarba dazasu samu ga talakawa fak'irai. suna dai fad'ane dan kar amusu dariya. Mama Fulani koda labarin yaje kunnenta saita ta6e baki tana murmushi k'asaita, Wanda ita kad'ai tasan fassarar kayanta. Tsaf yagama shiryawa zaije sashen da aka sauke abokansa a cikin masarautar, dan babu damar saukesu a 6angarensa, saboda angama masa gyara tsaf amarya kawai ake jira, su aunty Mimi ma dasuka kai lefe sun Sanar da amaryarsu kawai suke buk'ata, basai su Abba sun wahalar da kansuba wajen kaita da komai. Wannan dalilin yasaka aka yanke shawarar k'arama munubiya kayan munayar kawai, da safe za'aje a kuma jera mata su a gidanta😄. Cikin takunsa na kasancewar cikakken namiji mai tashen k'uruciya ga jinin mulki dake yawo ajikinsa yafito, waya ce manne a kunnensa, yayinda d'ayan hannunsa ke cikin aljihun jeans d'insa, bayi da hadiman gidan sai zubewa sukeyi suna kwasar gaisuwa, kansa kawai yake d'aga musu yayinda yake cigaba da wayarsa da Momma wadda tana India ita batazoba. Samha tak'araso gareshi a hanzarce, “Uncle ka tsaya mana please ”. ‘tayi maganar a shagwa6e saboda ganin ya basar da ita tamkar baima gantaba’. d'an juyowa yayi ya kalleta sannan ya d'auke idonsa yana cigaba da Murmushin sa na k'asaita saboda addu'ar da Momma ke jero musu ta zaman lafiya da samun albarka ta har abada acikin auren daza'a d'aura a gobe. jiyake tamkar yace Momma ta dainama auren shekara d'ayannan addu'a irin haka, shifa harma tausayi suke bashi yanda suke nuna farin ciki da zumud'insu akan auren, musamman idan ya kalli yanda masarautar tagama cika tab da dangi takowanne 6angare, ga tawagar wasu masarautu dasukayo gaba tun yau, hakama 'yan siyasa ba'a magana, dan ba k'aramar gayya papi da Sarki sukaima wannan aurenba, kasancewar shine jika namiji na farko dazaiyi aure a masarautar, Wanda kuma kowa ke saka ran shine magajin sarautar masarautar. Ita dai Samha tana tsaye tana kallonsa harya kammala wayar da Momma ya kashe. Had'e fuskarsa yayi yana hararta, “to maganatu miya faru kuma? kike kwalan kira tundaga wata uwa duniya?, wai sai yaushene zakiyi hankali Samha?”. Baki ta tunziro gaba, idonta harya cika da gwalla “amma dai Uncle aina fara yin hankalin ko, kumafa wani Abu Nazo na nuna maka, naje Sashenka wannan sarkin k'ofar yawanice kana wajen mai martaba”. Kansa kawai ya girgiza yana kallonta, saida takai aya sannan yace “to aini inada abunyi, yanzuma ba wai sauraren naki zan zauna yiba, dan nan ba India bane, ba'a ganina available ko yaushe OK?”. Harya juya zai tafi tarik'o hannunsa tana daddaga k'afafu idonta na zubar da hawaye. Kansa ya dafe domin sanin fitinar Samha, tace, “please Uncle Sam 2munutes to”. Juyowa yayi tamkar zai maketa, saikuma komi ya tuna ya fasa, d'an cije lips d'insa yayi yana hararta, “ke wai wace irin fitinanniyace ne?, Uwarmi to zaki fad'amin?”. Dariya tayi tana share hawayenta dan ganin tasami nasara, wayarta ta daddana sannan ta mik'a masa. Nanma Harar tata yayi kafin ya kar6a, itace yagani a photo da 'yammata biyu masu kama d'aya, kamarma yarinyar dasuke shirin auren contract, harya yatsina fusaka zaice suwaye? saikuma yatuna. d'an murmushi basarwa ya saki kafin ya kalli Samha da ta tsaresa da idanu. “Uncle ina aunty Munaya anan? ”. Wayar yamik'a mata yay gaba abinsa yana fad'in titsiye zakimin ma kenan? an fad'a miki bazan ganeta baneba?”. Baki ta turo tana k'unk'uni, “waikai Uncle Sam bazaka ta6a canjawa baneba? kai kenan kullum sai jan ajin tsiya, shiyya sama ALLAH yayoka jinin sarauta wlhy, Aunty Munaya kin bani da wannan mijin naki mai k'asaitar tsiya, aiko wlhy tunda kace haka saina had'a maka mugunta gobe a wajen dinner ”. Ta tuntsire da dariya saboda tuno mizata shirya masa. ★★★★★ *Rana bata k'arya........*⛹🏻‍♀ Yau mun wayi gari safiyar d'aurin aure, gida yakuma d'inkewa da jama'ar dukda d'aurin Auren na Azhar ne bayan sakkowa masallacin juma'a. Tun jiya banida lafiya, amma na hana su Ayusher fad'ama kowa, sai Magani suka samo min nasha, itama dai Munubiya duk sukuku take, babu abinda ke damummu sai jimamin rabuwa da juna, dan itama kusan zazza6inne ma ta kwana dashi, sai dai dayake nawa ya had'a da damuwa saina fita nuna jin jiki. Jama'ar gidanmu dai a harmutse suka kwana, wasuma ko barcin basu sami damar yiba saboda ciwon hasada dake cin zukatansu, gashi gida d'inke da jama'ar babu damar matsawa koda nan da canne sai an gane, bare sufita neman mafitar tarwatsa Auren, waddama suke d'an samin tallafinta kwad'ayinta yasaka canja shek'a (innaro🤣), dan jiya da suke zuba tijara shigowa tayi tamisu tas, harma tana Neman tone musu asiri gaban tawagar 'yan biki, badan gwaggo Safiyya ta lalla6a taba ba'asan inda jarabar innaro zata tsayaba kam. Ko karyawa ban iya tashi nayiba bare aje maganar wanka, ina kwance cikin bargo sai shar6ar kuka nakeyi babu wanda yasani. Ahaka gwaggo Safiyya tashigo kiranmu nida Munubiya, da k'yar su Ameera suka samu natashi zaune ina tangad'i, gaba d'aya nayi wujiga-wujiga dani, da taimakon Munubiya dake rik'e da hannuna muka iso gidan innaro inda su Abba suke jiranmu. Gaba d'ayanmu ne amaren aka had'a, abin mamaki saiga innaro ta kamani ta zaunar tanamin sannu, harda lallashina wai na kwantar da hankalina. Kowa zuba mana idanu kuwa yayi, su Fiddausi sai jan tsaki suke a zukatansu sunajin wata tsanar innaro aransu. Itakam bama tasan sunayiba, sai nannan takeyi damu nida Munubiya. Nasiha mai ratsa jiki da 6argo sukai mana sosai, muhimmancin aure da hak'uri, biyya da tsoron ALLAH, kare hak'in miji da k'yautatama danginsa da iyayensa, k'arfafa zaman lafiya a tsakani da rik'e sirrin miji, banda biyema k'awayen banza sukaika su baroka, musamman ma da dukanmu zamu cigaba da zuwa makaranta. Gaba d'ayanmu kowa hawaye yakeyi, musamman mani danakejin tausayin kaina dana iyayena dabasu San auren shekara d'aya nake shirin yiba nadawo garesu. Munci kuka sannan aka sallamomu, tunda muka dawo sai aunty salamah ta saka mu agaba dole mukayi wanka, da k'yar muka amince aka mana simple kwalliya, muka saka dakakken leshin da mama Rabi'a tasa aka d'inka mana cikin kayan biki dasuka mana itada innarmu, less d'in blue ne da fararen bet ajikinsa, sai aka nad'a mana d'an kwalima blue, munyi k'yau harma bansan yazan musalta ba, nan su Ayusher suka hau zuba mana pictures. lokacin 12 tama wuce, masallacin anguwarmu daza'a d'aura auren yagama cika dank'am da jama'a, dayake bashida nisa da k'ofar gidanmu. Cikin gidanmu kam ai ba'a magana, dan babu masaka tsinke, sai hayaniya kakeji wani bayajin zancen wani, rabin hirar jama'a kuwa duk akan zancen lefe nane da Wanda zan aura, wad'anda suka gani suna bama wad'anda basu ganiba labari. Su siyama dai koma ganinsu ba ayi, dan suna taya iyayensu kishi da hassada, aunty Ramla da aunty Raihana sai aunty Hauwa'u ne kawai suka shigo sukaima innarmu murna har d'akinmu, amma aunty khaleesa ko k'eyarta bamu ganiba, kuma tunda safe tazo gidan daga ita har zarah, matar yaa hameed ma mama hanata zuwa tayi, dukda tanaso tazo tama innarmu murna amma surukarta takasa ta tsare, gashi bama dad'in zaman 6angaren takejiba, saboda 'yan ubanci na dangin miji da aketa nuna mata, itama matar yaa Naseer tashigo, dan har picture mukayi da ita, amma matar yaa Shafi'u ma bata shigoba. Hakan duk bai dameniba, dan ni yanzu basune agabana ba, damuwata tarkon dana saka kaina na auren contract shike cazan tunani a halin yanzun, Wanda ko munubiya nakasa sanarma gaskiya lamarin. *_1:30pm_* Masallacin yagama cika taban mamaki, tuni tawagar gidan Sarki sun iso tun bayan gama sallar juma'a, d'aurin aurene daya tara manyan mutane ta dalilin gidan sarauta, manyan sarakunan k'asarnan da 'yan siyasa, governors senators attajirai na gida dana k'etare, talakawan gari da tawagar iyaye da dangin sauran angunan, abokan su abbanmu danasu yayunmu, abokan anguna da abokan arzik'i, dangin iyayenmu mata danasu abbanmu, kowa ya hallara, bakajin komai sai kad'e-kad'e da bushe bushe irinna gidan sarauta. president da Kansa ya iso wannan waje bisa gayyatar papi, bansan yanda zan musalta muku irin cikarda anguwarmu tayiba aranar, bama zaka iya gane taka maimai inane ake d'aurin aurenba. Su Kansu masarautar su Galadima sunsha mamaki, basuyi zaton auren Na Galadima zai tara jama'a manyan mutane hakaba, dubi da yanda ba d'iyar wata hamshak'iyar masarautar zai auraba. basu San abin ba anan yakeba wai *d'uwawu yafi fuska k'yawun gani*🙊🤥😜😂 inji masu iya magana......................✍🏼 Amin afuwa, mu had'u tomorrow danjin yanda d'aurin aurenba zai kaya⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Barkanmu da dawowa😄✋🏻🤝🏻 *_ya ALLAH ma gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣0⃣ .........A cikinmu Fauziyya ce babba, dan haka aka fara d'aura auren ta, daga nan sai ni da Munubiya, an fara d'aura na Hassana Auwal fharuk (munubiya) da yaa marwan Ibraheem, sannan ni Hussaina Auwal fharuk (Munaya) da Muhammad Sameer Saifudden Abubakar (Galadima), saikuma Safara'u, sai Haleematu, Fiddausice k'arshe. Ana gama d'aurin auren busar algaitu suka fara tashi, sarkin marok'a yafara zuba kirari wa Ango Galadima sarkin gobe a masarautar gagara badau. Maganar k'yawun da Anguna sukayi ma 6ata lokacine, kowanne yafito angonsa sak abin kallo da birgewar kowa, duk miskilancin yaa Marwan saigashi yana washe hakwara tamkar gonar audiga😁. 🤥ance anguna basa kuka ranar aurensu, to kuwa yau saiga Galadima na share hawaye, dukda auren contract yayi nakuma shekara 1 kacal, saiyajisa wani iri daban, ya kuma zama babban mutum, tuno Abie dayayi yasaka hawaye fitowa daga idanunsa, bazai iya tuna tsawon lokacin dayayi kuka na k'arsheba, amma saigashi yau yanayi acikin d'umbin jama'a, akuma ranar d'aurin auren da ya rad'ama suna na (wucin gadi). Papi ne yad'an bugi kafad'arsa yana murmushin jin dad'i shima, dajin wata k'aunar jikan nasa ta musamman. Aikam masu videos da photuna ansamu abinyi, hakama masu d'auka awaya ba'a magana. Kafin kace mi social media ta d'auka, lungu da sak'o hotunan d'auren aurenne suketa yawo, musamman da jama'a ketajin wai wadda aka bugasu a jarida yana kissing ce ya aura, wayyo ALLAH abin magana yasamu a yanar gizo, kowane polder na charts ka shiga zancen kenan dai. Daga wajen d'aurin aure tawagar gidan su Galadima k'aton hall d'in da aka tanada domin cin abincin bak'i suka nufa, duk wani maiji da kansa zaka sameshi awajenne, Galadima har kansa yafara ciwo saboda yawan magana ta amsa gaisuwar jama'a da murna da yakeyi. Ana tsaka da cin abincin Momma ta kirashi, dama shi ba ma abincin yakeciba, zaune kawai yake yana juya spoon a plate, wayarsa yaciro daga aljuhun gaban rigar milk d'in shaddarsa, dan tuni yacire malum-malun d'in tana hannun Harun. Ganin Momma yasashi mik'ewa yafice daga hall d'in gaba d'aya, can waje yasamu wasu kujeru ya zauna sannan yakirata ta video call, tana d'agawa sai kawai ya fashe mata da kuka ganinta zaune kusada Abie. daga Momma har Abie d'in sagade sukayi suna kallonsa, saida yayi mai isarsa yasaka handkerchief d'insa ya goge fuska sannan Momma tace “ho d'an nema duk murnar aurence kokuwa shagwa6a ce ta motsa?”. Tur6une fusaka yayi zai sake wani kukan Momma ta kwashe da dariya irin wadda yadad'e baiga tayiba, Abie ma murmushin sane ya fad'ad'a sosai. saida Momma tayi dariyar mai isarta sannan tace, “Muh'd kafa girma, kai yanzu babban mutumne, nan kuma da wata shekarar kazama baba, amma katasamu gaba kana kuka?”. Handkerchief yasaka yakuma goge hawayen dasuka taho masa, sannan yace “momma na barka da rana”. “Barkan ka dai angon d'iyata Munaya, ALLAH ya sanya alkairi yabada zaman lafiya yasa bad'i iyanzu munan muna shagalin sunan jikan mai martaba”. tayi maganar tana kallon Abie daketa zuba murmushi, gira d'aya ta d'aga masa, shikuma ya k'yafta mata idanu. Dariya Galadima yasaka musu, irin wannan soyayya haka summa manta dashi. Gyaran murya yayi sannan Momma ta d'ago tana kallonsa, suka saki dariya lokaci d'aya. yayinda Abie ke tayasu da Murmushi. Galadima ya tsagaita dariyar yana fad'in “my Abie ya jiki?”. Da idanu Abie ya amsa masa da Alhmdllh, sannan yamasa nuni da ALLAH ya Santa alkairi. Hannu yasa yarufe fuskarsa alamar jin kunya. Har aka kammala liyafar cin abincin yana a waje suna hira da parent d'insa, saida papi ya aiko akirasa saboda yanason nunashi wa jama'arsa da basu sanshiba, hakan yabama wasu daga cikin 'yan masarautar su haushi, sai dai basuda yanda zasuyi da wannan tsohon mai k'arfa-k'arfar tsiya da Nuna Isa. Bayan ya Yanke call d'in yamik'e yabi bayan d'an Aiken, ya iske a hall d'in kuma papi ya had'a wani video call d'in dasu Momma, domin Abie yaga d'umbin jama'ar dasuka halarci d'aurin auren gudan jininsa. Aiko yaji dad'i sosai harma Momma, harda hawayen farin ciki Abie yayi. Nandai a kaita zuba masa addu'ar Neman lafiya ga mummunar addu'a ga dukkan masu hannu na shigarsa wannan halin tsawon shekaru, da idanu yake fad'ama Momma magana itakuma tana fad'a musu. Daga nan Galadima yayi jawabin daya ta6a zukatan jama'ar wajen, wasu harda share hawaye, wasu daga cikinsu dasuka San wasu abubuwan daya faru wa tsohon sarki Saifudeen kam duk sai zukatansu suka karye, musamman masu hannu aciki dasuka bada gusunmawa, jin addu'a da alwashin d'ansa Muhammad Sameer dake tabbatar da bazai bar duk mai hannu acikiba, sai dai shima amasa irin na mahaifinsa, hakanne kawai zai iya dakatar dashi. Abie da Momma Kansu kuka sukeyi daga can suma. Taron yatashi zukatan wasu cikeda tausayin Galadima da k'udirin taimakonsa, yayinda yasamu k'yaututtuka daga manyan k'asar. Masu hannu aciki kuwa suntafi da nufin sake shiri akan Galadima d'in, domin aganinsu sunyi sake d'an zaki ya girma, kuma Galadima na neman zame musu *RAINA KAMA......* ★★★.★.★.★★★ Gidanmu kam tunda aka kammala d'aurin aure labari ya shigo gabana yashiga luguden daka, rungume juna mukayi ni da Munubiya muka fashe da kuka mai ban tausayi, Wanda muka saka jama'a dayawa kukan, ciki kuwa harda Innarmu da mama Rabi'a. babu wanda yace mu bari, aka barmu mukayi mai isarmu, dan kowa yasan dolene muyi irin wannan kukan na rabuwa, dan yau babu fashi dolene mu Rabun, abinda baita6a faruwa agaremuba, kullum a gado d'aya muke kwana muke tashi, kowanne aiki tare mukeyin sa, komai namu iri d'ayane, daidai da pants & bra iri d'aya muke sakawa, idan d'aya bashida lafiya saika d'auka muduka bamuda lafiyar, babu abinda ke banbantamu sai hali, amma yau gashi aure zai banbantamu, jinai inama muma mazane tamkar su Aiyaan, yanda babu mai rabamu d'in. Haka dai wannan yinin biki akayishi a wani iri, mu cikin damuwar rabuwa, matan gidanmu cikin hassada da bak'in cikin mun fisu. danma Su Abba sunyi dogon gargad'i akan wlhy duk wacce tasake tada finina a gidan sai dai ta k'arasa bikin a gidan su. Wannan furucinne yasaka kowa yin likimo, sai dai fa ta ciki na ciki🙊😂. Hotunama da akayi na family wasu fuskar tasu tamkar kashin farar safiya😖🥴, Innaro kam ai mune nagaban girarta a yau, sai dama-dama takeyi damu, dama komai akayi saitace an kaima Ai'sha dai ko, (😂su innaro anga banza). Wannan abun datakeyine keta kuma hasala matan gidanmu da 'ya'yansu, itakam ko a ha6ar kallabinta, warkajaminta kawai takeyi na murnar auren jikoki. Yayinmu mazane kawai babu ruwansu, duk suna cikin farin cikin wannan aure. Bayan la'asar sakaliya saiga sak'o daga masarata mutane biyu d'auke da akwatina biyu wai sun kawo kayan da zansa awajen dinner ni da Munubiya, sun shirya dinner d'inne mu biyu kawai banda sauran amaren. Wannan lamari kam ya sosa zukatan mutane da yawa, ni kaina banji dad'in hakanba gaskiya, dan banason su d'auka kamar mun banbanta da sune yanzun, gaskiya da ace inada Number Galadima dana kirashi nace a fasa wlhy, saboda muma anan gidanmu yayunmu sun shirya mana dinner d'in gaba d'ayanmu, duk da ni dama ban saka ran zuwan Galadima ba a wajen. Gashi kuma gate pass guda 30 kacal suka kawo, alamun basa buk'atar mutane dayawa a wajen kenan, ikuma na nace inhar bada sauran 'yan uwana ba ban zuwa nima d'in. Lallashin duniya anyi nak'i sauraren kowa, nakafe akan bazan jeba. Matan gidanmu kam cewa sukayi munafurcine kawai. Zancensu bai dameniba, nidai ina akan bakana bazanjeba. su Ayusher sun rasa yanda zasuyi dani, dama akwai number Galadima saisu kirasa su sanar masa halin da ake ciki. Innarmu kam ko k'ala batace daniba, yitaima tamkar batasan mi akeyiba, mama Rabi'a da Aunty Salamah sai fad'a sukemin kamar zasu dokeni, hakama innaro, sai jaraba takemin harda dungure min kai. cikin ikon ALLAH kuwa ana cikin haka saiga kiran Samha yashigo wayata, Ayusher ta d'auka suka gaisa, azaton Samha nice, saboda muryar Ayusher ma tana kama da tamu. Tace, “Aunty gimbiya ya hidima?”. Murmushi Ayusher tayi danjin sunan nawa harya canja, tace “ba ita baceba Ayusher ce”. Cikin jimami tace Aunty gimbiyar fa?”. Labarin komai Ayusher tabata, sannan tace “dan ALLAH ko zaki had'ani da Galadima?”. Samha tace “babu damuwa bara na dubashi, duk da nasan yana tare da abokansa yanzun”. Godiya Ayusher Tamata sannan suka yanke wayar akan idan tagansa zata kira”. Masifa nahau yima Ayusher akan miyasa zatace saita fad'a masa, nidai koma miye babu inda zanje. Banza Ayusher tamin tamkar batasan inayi da itaba ma. Kusan muntuna 7 saiga kiran Samha yasake shigowa, Ayusher ta d'aga, maimakon taji muryar Samha saitaji ta Galadima cikin k'asaitar nan tasa da izza. Nutsuwa Ayusher tayi sosai ta gaisheshi, sannan ta masa bayanin komai. uffan bai ceba saida ta kai ayar zancenta, lips d'insa yad'an cija kafin yace “had'ani da ita”. A kunne Ayusher ta sakamin wayar, yayinda kowa yafice daga d'akin aka barni ni kad'ai saikace wata mayya. Dagani har shi kowa yayi shiru, shi yanajin kansa nima hakance, kusan minti 4 yaji banida niyyar tankawa saiya yi guntun tsoki, “shin ke baki iya gaisuwa bane?”. Dukda naji ban k'yautaba saina ta6e baki, cikeda dakiya nace, “ina yini”. muryata a dishe take saboda kukan danaketa sha tun jiya. Bai amsa gaisuwarba yace “wane sak'o kika bada a bani?”. Saida na tunzuro baki sannan nace “yoni minace abaka?”. Lips d'insa ya lasa yana fad'in “nikikema wannan abun?”. Banza namasa danni bansan mina masaba kuma. Yaja guntun tsoki, “ki kama kanki fa, karkiga auren contract mukayi, akwai sharid'd'a acikinsa, bana buk'atar ganin kowa awajen inba keda sister d'inki ba, haka na tsara, kuma babu mai canjamin ra'ayina, zuwa anjima wadda zata shiryaku zatazo, idan kin gadama karki bari a shiryaki, nikuma zakiga mi zan yi akai..”. d'if ya katse wayar, cirota nayi daga kunnina ina dubawa tamkar zan ganoshi acikinta. naja tsaki ina fad'in “aikin banza kaje ka koyo R sannan kamin wannan ikon, nifa baka isa takani ba acikin auren contract...... ” Sauran maganar ta mak'ale a mak'oshina saboda shigowar munubiya. Zama tayi akusa dani, “sweetheart zan iya neman alfarma a wajenki?”. Kai na d'aga mata. Ta gyara zamanta sosai tareda kamo hannayena duka acikin nata. “inason kima mijinki biyyay kiyi yanda yakeso, yanzu hakkin bin dokarsa tarataya a kanki dole inhar bata sa6ama addini ba, kina kaucewa kuwa zaki had'u da fushin ALLAH, tunda yace haka yakeso ayi kiyarda kawai, awa nawane anyi an tashi kowa yakama gabansa”. Alk'awarin Dana mata yasani amincewa zanje tilas amma badan raina yasoba. An tsara wad'anda zasuje, dan haka aka damk'ama kowa gate pass d'insa a hannu ya Adana. dukda wasu gani kwaf zasuje kuwa. Bayan sallar isha'i saiga masu mana shiri sun iso, babbar magana wai d'an sanda yaga gawar soja. Jama'a ni kaina bamma gaskata cewar nibace ballan tana Ku 'yan kallo, saika rantse kace dama can mud'in jinin sarauta ne, munyi k'yau har mun gaji, gashi dandanan akayi aka gama, har kusan 9pm muna jiransu, gidan yayi tsitt duk wad'anda zasuje dinner sun tafi, wad'anda zasu bimune kawai tare damu muna jiransu Galadima, dan shima yaa marwan d'in baikai ga isowaba. Sai around 9:15pm sannan mukaji dirar mitoci a k'ofar gidan. Aunty Mimi ce da kanta tashigo itada wasu bayi guda hud'u, saida ta gaisa dasu innarmu sannan aka mata iso d'akinmu, wani dad'ine ya ratsa zuciyarta, dukda batasan wacece matar k'anin nataba acikinmu, amma muntafi da imaninta, jitai inama natane wad'an nan twins, ALLAH yasa haihuwar farko na haifo musu irinmu. Daga ni har munubiya rissinawa mukayi muka gaidata cikeda girmamawa, dan munsan a haife ta haifemu, dukda bawai sa'ar innarmu bace, ko mama Rabi'a ma ta girme mata. Hakan damukayi yamata dad'i kuma mun birgeta, ta kama hannayenmu tana yaba k'yawun damukayi, wasu turarurruka ta fidso kala uku a bag d'inta tashiga feshemu dasu, dukda uban turaren da aunty salamah tamana wanka dasu zance, dan itama haka taita zazaga mana su d'azun, ni saima hawarmin kai sukeyi wlhy. Wasu alk'yabbu masu azabar k'yau iri d'aya aka saka mana, takalman dake k'afarmu kansu abin kallone. Aikam bamu fitaba saida tamana hotuna, afaloma saida aka mana muda su innarmu. A waje muka iske motoci guda uku masu k'yau, da alama sauran motocin sun d'auki jama'a sun tafi. Saida mukaje jikin motocin sannan aunty Mimi tayi murmushi tana kallonmu, to karnayi abin kunya, wacce ta my k'ani? wacce ta Marwan?. K'asa mukayi da kanmu saboda kunya, saida ta kuma maimaita tambayar sannan munubiya tayi k'arfin halin nunani, kunyarmu takuma birgeta sosai, hannun munubiya ta kama tana fad'in kece babba ai, zoki fara shiga”. a motar farko ta sakata, sannan tadawo takama hannuna ta sakani a ta biyu. Rufe k'ofar tayi takoma motar bayanmu tashiga. yayinda kuyangin nan hud'u suma suka shiga motar k'arshe. Tunda nashigo k'amshin turarensa yadaki hancina, ta gefen ido na saci kallonsa, kishin gid'e yake a kan kujerar motar tamkar yasamu gado (dan bansan yama zan musalta muku tsarin motarba nikam, ammafa komai abin kallone) k'afarsa d'aya a k'asa d'aya akan kujerar, kansa na gab dani, dan dazai zame ko motsawa dolene saiya ta6a jikina, sanye yake cikin wasu Fararen suit masu azabar k'yau, sunyi mugun fidda ainahinsa matsayin cikakken namiji mai aji da gayu, aikin danna wayarsa kawai yakeyi tamkarma baisan na shigo motarba, dan ko sau d'aya bai d'ago ya dubeniba. Nima basarwa nayi nayi tamkar bansan dawata halitta acikin motarba bayan driver. Shikuwa tun shigowa ta k'amshin turarena yabigi hancinsa tareda shiga magudanar jininsa, a rayuwa yana matuk'ar k'aunar k'amshi, lumshe idanunsa yayi yana lasar lips, amma jinkai da k'asaita ta hanashi d'agowa yako dubeni. Itakam munubiya tana shiga bayan aunty Mimi tarufe k'ofar yaa marwan jawota yayi jikinsa, tareda sumbatar gefen kumatunta. ta matse jikinta waje guda saboda tsorata, muryata na rawa ta gaidashi. Ya amsa yana wani kuma shinshina wuyanta da bata wasu kisses d'in. Mamaki da al'ajabine suka kamata, anya kuwa wannan yaa marwan d'in nanne mai shegen muskilanci da share mutane?, kanta bai ida kwancewa ba saida taji hannunsa indama batayi zatoba, tamkar zatayi kuka tace “please yaa marwan kayi hak'uri dan ALLAH, cikin motane fa”. Rungumeta kawai yayi batareda yayi maganaba. A wannan yanayin mukaji motocin sun tsaya. Bayan an bud'e mana duk muka firfito, tsakanina da Galadima kuwa babu Wanda yacema wani kanzil har muka fito. Yaa marwan da Munubiya ne agaba rik'eda hannun juna, saini da nawa d'an hayak'in Mr k'asaita abaya, harmun fara tafiya Aunty Mimi tamasa magana. banji mitace ba saboda da Indianci tayi maganar😜. Jinai kawai wani lallausan hannu cikin nawa, dagani harshi babu shiri muka kalli juna saboda shock d'in daya jamu a time d'aya. Shine yay azamar janye nasa idanun yana cije lips, kafin nima na janye nawa cikeda kasala da luguden zuciya. Mamakine ya kamani lokacin da muka shigo hall d'in, inda sauran 'yan uwanmu sukene Ashe, sainaji dad'i sosai wlhy. Nandanan mc yashiga sanar da isowarmu, tunda muka shigo kallo gaba d'aya yadawo kanmu, musamman mutane dake son ganin Galadima a yau. Can saman hii table muka isa muma, mazaunin daya kasance namu, su Safara'u tamkar su saka ihu saboda ganin yanda muka had'u tamkar bamuba, duk sai suka raina nasu kwalliyan dukda suma sunyi matuk'ar k'yawu kuwa.. Bayan mun zauna angunan suka taso suna kawo gaisuwa wajen Galadima, fuskarsa d'auke da murmushi yake amsa musu tareda mik'a musu hannu suyi musabaha, koda sun nok'e saiya kamo hannun nasu da kansa. Bak'in ciki tamkar yakarsu Halimatu, ganin angunansu suna kai gaisuwa wa Galadima, basusan hakan dole bane agaresu kodan kasan cewarsa d'an masarauta wandama ake da yak'inin zama sarkin gobe idan da rai, idanma badan hakan ta kasanceba ta ina suka Isa ganinsa balle ma har suyi gaisuwar Baki da baki harda musabaha. Aishi adaline ma tunda harya iya halartar taron nasu. Yayunama duk saida sukazo suka gaisa dashi, mazan da matan, sannan mukayi hotuna, su Zarah da siyama matan 'ya'yan senator kam ai yau saikikaji tsit babu felek'e, dan mazajen nasuma ko zuwa basuyi wajenba, kamar yanda basu halarci tasu dinner d'inba lokacin aurensu. Aunty Mimi dakanta ta kar6i microphone tabada hak'uri da neman alfarmar tafiyarmu, saboda suma mutanensu nacan suna jiran isowarmu, dama munzone domin kar6ar excuse. Hakkane yad'an rage fushin wasu, sannan mun tafi dawasu acikin yayunmu maza. Mun tafi kowa yana yaba tsarin namu. Yanzuma haka muka tafi tamkar wasu kurame, saidai yanzu a zaune yake, yajingina kansa da kujera ya lumshe idanu. Nikam gefe na maida kaina ina kallon titi. Yanzun kam koda motocin suka tsaya bamu fitaba, sai kusan mintuna 10, Ashe lokacin harsu munubiya da yaa marwan sun shiga, saura mu kuma. Bamu fitoba saida akayi knocking glass d'in gefensa, ahankali ya sauke glass d'in batareda ya bud'e idonsa ba, wanine yalek'o yana fad'a masa mu fito, duk bud'e mana motar akayi dagani har shi sannan muka fita. Zagayowa yayi inda nake tsaye, a mamakina da al'ajabi sai kawai naji ya sak'alo Hannunsa a k'uguna, cikeda firgici nad'ago na kallesa, saiya sakar min harara dawani munafikin murmushi, saika rantse da ALLAH kallon soyayya yamin, nikam dukda kwarjini dayamin saida na turo baki gaba da hararsa a kaikaice, ALLAH ma yasoni baiga hararba. Ahankali muke tafiya saboda Alk'yabbata, yayinda kuyangin ke watsa wasu flowers masu k'amshi a inda zamu taka, aunty Mimi kam da wata daban santaba suna feso mana Abu mai k'amshi. Kai jama'a wajen taronnan fa ya had'u, k'arshen had'uwa kuwa, an k'awata wajen da kwalliyar white and Golden colors, yayinda kwalliyar jama'ar wajenma white and Golden colors ne, (suma mutanemu dasukazo wajen dama ankawo musu kaya irin kalar). Mazan sunsha wankan white suit, takalmansu da agoguna zuwa tie duk golden, matan kuma white gown ta material sai d'ankwali golden. Yayinda tamu shigar ta kasance golden gaba d'aya, su Galadima kuma sun saka white suit, komai nasu white ne shida yaa marwan. Tunda muka shigo wajen ya d'auki tafi, yayinda aka saki wak'ar da aka raira domin mu. (Bara nad'an raira muku kad'an🤥😜). *_Alk'awari yacika munubiya alk'awari yacika.... yacika yacika munaya alk'awari yacika amarya...._* 🙄iya nan na iya to🥴⛹🏻‍♀ Gaba d'aya sai wani tsoro da kunya ya kamani, nafara tafiya ahankali tamkar kazar da kwai ya fashema aciki. Bansan lokacin da Galadima ya rankwafo kainaba, dan tunanina yatafi wajen mamakin yanda suketa shiryama auren shekara 1 wad'annan bidi'oin. Jinai kawai an d'aukeni cak, ihu kawai aka sanya awajen da uban tafi, yayinda aka kuma sakin sabon kid'a na musamman. Runtse idanuna nayi kawai zuciyata na kai kawo tamkar zata fito waje saboda mamakin munafuncin Galadima. (Yo inba munafuci ba miye na d'aukata agaban jama'a, bayan ni da shi ko magana bata had'amuba😏). Bai direniba sai a kujerar da aka tanada domin mu. Anan d'inma zama yayi yasakani jikinsa, kunya da haushi duk sun cikani, wlhy badan karna kunyatashi ba dayasha mamaki. Gashi sai wani magana yakemin k'asa-k'asa kai kace ta arzik'ice, nanko duk gargad'ine wai na kama kaina karnayi abinda wani zai fahimci ba auren soyayya bane a tsakaninmu. Baki na tunzuro gaba dan haushi, yasaka d'an yatsa ya d'alli bak'in nawa. Naji zafi wlhy kuma.😏 Abun ALLAH wadai bai k'areba saida akazo yanka cake, bayan su munubiya sun gama nasu cikin mutunci da yaa marwan saimuma muka yanka namu, maimakon yabani kamar yanda na bashi sai kawai yasa Wanda yaciro a bakinsa, bayan yayi tamkar zai bani, harna bud'e baki zan kar6a saiya lunk'uma a baki, nanma mutane suka Sanya dariya da tafi. Wai kawai ina hararsa saboda haushin abinda yayi sai kawai naji fuskata cikin tafin hannunsa, kafin nayi wani yink'uri ya had'e bakina danashi waje d'aya yajuyemin cake d'in daya gama narkewa da yawunsa a bakinsa. Bai cire bakinsaba saida ya tabbatar na had'iyeshi sannan. Ai wlhy ihun yanzun yafi na ko yaushe, abokansa harwani kirari suke masa, yayinda wasu keta d'auka a hotuna, Munubiya kanta kunshe fuska tayi a alk'yabba tana dariya, duk miskilancin yaa marwan saida ya dara shima. Aikam saida nayi hawayen bak'in ciki, mugu kawai yabani k'azantar yaunsa nasha, wlhy badan mutaneba saina k'ak'aro amai kuwa. Daya bani drink ko k'insha nayi, ya rankwafo kaina bakinsa saitin kunnene yace, “bakiji sharad'inaba kenan? ALLAH shima zan zuba abaki na juye miki shi a bakinki yanzunan. Ai babu shiri na kar6a kuwa. Daga nanne Samha taje wajen mc ta kar6i microphone wai tanason saka gasa tsakanin Uncle Sam da Uncle marwan, za'a shigar damu wani d'aki, bayan mintuna biyu mu fito, kowa ya nuna matarsa, duk wanda ya canka dai-dai shine yaci gasar, shikuma zata bama k'yautar. Galadima jiyay tamkar ya mangare Samha, sai antaya mata harara yakeyi itada Sauban, dan yasan wannan munafurcin sune suka kulloshi. Ai kam k'in kallonsa sukayi sunata k'unshe dariya. Dole yanda sukace d'in haka akayi, muna shiga aka gyaramin janbakina da Galadima ya tsotse, sannan aka kuma feshemu da turararurruka saboda kowance k'amshin turaren mijinta daya manne mata yabar jikinta. Kujeru aka ajiye mana muka zauna, kowacce taci serious. Da Galadima aka fara, gabansa sai dukan sittin-sittin yakeyi, danshi da gske ba iya gane ni zaiyiba, inba na nuna halin nawa bane. Aiko ya nuna d'aya acikinmu, mik'ewa tayi takoma gefensa ta tsaya, amma bai ta6a ta ba, dan ba'asan wacecenba acikinmu. Shima yaa marwan rikicewa yayi, dama mafi yawan lokuta ta halayya yake ganemu, shima dai wadda Galadima yabari ya nuna. Bayan suma sun koma gefe aka koma kan za6in Galadima, mc yace “zamu iya Sanin wacece?”. Murmushi munubiya tayi, cikin sanyinta tace “Munubiya ce”. Juyowa Galadima yayi ya kalleta, sanyinta ma kawai ya isa tabbatar da gaskiyarta. Nima aka tambayeni cikeda Jan aji nace “Munaya ce”. Nanama ihun akayi, cikinsu babu Wanda ya canka dai-dai, dan haka ni da Munubiya su samha suka bamu wata k'yauta dabamusan ko miye a cikiba, wai mune mukayi wining. Daga nan aka rufe taro da addu'a aka tashi. Har gida suka maidamu muda tawagarmu, lokacin 1:15pm. Muna zuwa kowa makwanci kawai ya nema...............✍🏼 Irin wannan dogon page haka😨🙆🏻, shikenan harda na gobe na had'a muku kenan🙄. ⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ *_Ya ALLAH ma gafartama iyayenmu_*👏🏻😭 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣1⃣ .......Har safiyar yau jikina sai k'amshin turaren Galadima yakeyi, feena dake kwance kusa dani tace, “Mrs Galadima! k'amshin nan nakufa yayi over”. Harara Na dalla mata, tareda kai mata bugu ta kauce tana dariya, Bilkeesu ma dariyar takeyi, ta jawo wayarta tana fad'in “jama'a kunma tunamin, bara na duba comments d'in jama'a akan pictures d'in jiya”. Zumbur natashi zaune ina kallon Bilkeesu, “Bilkeesu kinada kai kuwa? yanzu nan hotunanmu kika mik'ama duniya?”. Da sauri Ameera tace, “to miye aciki, ai gamma mak'iya masu yad'a hotunan wancan 6atacin har 6utiyarsu Na rawa sugani yanzu kin zama halalinsa, ai wlhy jiya kusan kwana nayi karanta comments d'in jama'a akan pictures d'in, idanma mu bamu turaba wlhy abokansa sun yad'a a kowacce kafar yanar gizo, kuma yarinya harma a news wlhy an nuna, idanma baki saniba live aka nuna komai awasu gidajen tv”. Hannu na d'ora aka kawai nafashe da kuka saboda bak'inciki, nace “dan ALLAH harda abinda yaymin?”. “sosaima kuwa”. ‘cewar Ameera’. Kukana yakuma k'arfi sukuma suka saka dariya harda rik'e ciki sukeyi, nikam wlhy kukan gaske nakeyi basu saniba. Munubiya ce ta fahimci hakan, saita rungumeni tana k'ok'arin rik'e dariyarta data kasa rik'uwa. Ahaka aunty salamah tashigo tasamemu, “kai lafiyarku kuna dariya kuma ita tana kuka?.” Labari suka bata, ita kanta dariyar tayi, “yo miye abin kuka anan, koba komai ai ya nunama duniya yana k'aunarki, 'yan bak'in ciki kuma yasaka musu ciwon zuciya”. Kallonta nayi ina shar6ar hawaye, “yanzu nan aunty salamah kema haka zakice? mutum yamin wannan iskancin a bazama duniya sannan kuringa d'aukarsa abin kirki? yanzu dan ALLAH idan su Abba suka ganifa? tunda ance harma gidajen TV aka nuna”. “kajimin yarinya, yo ina kuma ruwan su Abba, mijinki nefa yanzun, to ai su inna ma duk sun gani agida, haka suma su abban”. Zumbur nayo tsalle tsakar d'akin hannuna bisa kai nace “galadima ka kasheni wlhy, ka cuceni ALLAH ya isana”. Dariyarsu k'aruwa tayi, suka shiga yi harda hawaye. yanda kukasan Na bibbigesu haka nakeji. Aikam yinin ranar ban yarda Na had'a ido da kowaba agidanmu, har lokacin da innarmu suka kiramu sukai mana fad'a itada mama Rabi'a da inna lami. Munci kuka tamkar zamu k'arar da hawayenmu. Zuwa la'asar fa anfara shirin kaimu gidajenmu, saifa lokacin hankalina dana Munubiya yakuma tashi sosai, domin abinda ake gudun yazo (rabuwa😭, sabo turken wawa). Muna d'aki nida munubiya kowa zazza6i ya rufeta, yayinda iyayenmu keta k'imtse-kimtse, ita kanta innarmu jikinta yayi sanyi lakwas, saboda ganin abinfa da gaske ake, tafiyar zamuyi mu barta. Suma sauran amaren kowacce Na d'akin uwarta, wasunsu kam ko'a jikinsu, hankalinu kwance Dan d'okin auren sukeyi su. Anayin sallar magriba inna lami tazo tasakamu mukayi wanka, ana shiryamu muna kuka, bayan mun saka atanfa iri d'aya da aka bamu da gyale aunty Salamah tafara zazzage mana turarurruka ajiki. Duk wasu tarkace an had'a manashi kowa a handbag d'insa, sannan aka tarkatamu dukkan mu amaren zuwa falon Abbanmu, dukkan iyayenmu mata suma suka shigo, harda innaro da gwaggo Safiyya. Nasiha aka shiga mana mai ratsa jiki, mukam sai shar6ar kuka mukeyi mu dukanmu, hakama iyayenmu mata bakowa ya iya yimana nasihar ba. tun ana mana fad'an naji ana rad'e rad'in isowar wasu daga cikin angunan, wani kukan bak'in cikine Yakuma tahomin saboda tuna ni nawa Auren nanda shekara 1 ya k'are. Rungume innarmu mukayi yayinda akace mufito masu d'aukar amare duk sun iso. Innarmu Itama kukan takeyi, da gyar aka ciremu daga jikinta, an fara fita dasu fiddausi saboda motocin d'aukarsu duk sungama isowa, nice dai basu isoba. Suna kuka da komai aka fita dasu, yayinda dangin iyayensu mata kowa tabi tawagar mortar tasu amaryar, danginsu abbanmu kuwa rarrabuwa sukayi, domin su sami zuwa kowanne 6angare suma. Motocinsu Na fita daga anguwar na gayyar abokan Galadima suka shigo, mitocine a Jere kuma masu yawa, abokan yaa marwan ma dama su suke jira, dan ance dole sai Munubiya tamin rakkiya sannan tunda nice k'arama. Bushe-bushen algaita yafara tashi anguwar tamu, dukda darene hakan bai hanasu busa kayarsu ba, hakan ya tabbatarma da 'yan anguwa tawagar gidan sarauta sun iso kenan. Mata hud'u sun shigo gidanmu tareda kuyangi, Alk'yabba mai azabar k'yau da suka kawo aka sakamin, sannan aunty salamah takuma fesheni da tirare dagani har Munubiya. Da k'yar aka 6an6aremu daga jikin innarmu, tana kuka munayi, haka aka fita damu k'ofar gida wajen motoci. Motar datafi kowace tsari da k'yau aka sakamu nida munubiya, sannan inna lami da gwaggo Safiyya suka zauna a gefenmu. Kuka muke rik'e da hannun juna, har aka Isa damu cikin masarauta. Mom itace zaune a matsayin Momma uwar Ango kenan, Dan haka aka kaini sashenda take tareda dangin Momma. Tarba ta mutunci aka mana, irin wadda kowad'anne iyaye suka kai 'yarsu gidan wani aka mata wannan tarbar hankalinsu zai kwanta sosai. Su inna lami basu wani dad'eba suka fara mik'ewa, saboda suna son mik'a Munubiya itama. K'ak'a rak'a k'aka, yanzufa akeyinta, danni da Munubiya mun rik'e hannun juna gamma munk'i saki, anyi lallashin da ban magana amma munk'i, da k'yar aka rabamu muna kuka tamkar ranmu zai Fifa. mun burge jama'a da basu tausayi sosai, sai hotuna ake zuba mana kuwa a wayoyi, (yo gidanne kwanyar da lantarki ko ina🥺💡). Mom tasakani a jikinta tana lallashina da bani hak'uri, bayan fitarsu aka kaini wani d'aki, har lokacin ina shashshekar kuka, su Ayusher duk suna tare dani, basubi Munubiya ba, dan sunsan ita yau yaa Marwan zai shiga daga ciki🙊😎😜. Har lokacin mom Na tare dani, zazza6ine mai zafi yarufeni kuwa, amma dukda haka saiga wata mata wai tazo shiryani, Ashe za'ayi Mother's event ne acikin gidan dakuma wanu Abu dasuke kira wai tarbar amarya a masarautar. Babu yanda zanyi, haka Na zauna tamin kwalliya Na shirya cikin less lemon green, aka sakamin alk'yabba mai k'yau itama, yanzuma har hular aka sakamin, Dan haka fuskata arufe take, saina sami damar yin kukana hankali a kwance. Mom da kanta tazo ta kama hannuna muka fita, yayinda kuyangi ke binmu abaya. Filine aka k'awata da haske, anmasa decoration da kayan sarauta Na kwalliyar gida, anutse kowa yake zaune, babu wata hayaniya sosai, (abinka da lamarin manya to🥳). Yaukam Galadima cikin ainahin basarakensa yafito, domin komai Na jikinsa Na sarautane, yasha alk'yabba kalar tawa, sai dai tasa ta maza ce, hard'e yake a zaune bisa wata kujera 2sita, wlhy wanda baima saniba saiya d'auka sarkinne gaba bad'aya, yaci mur fuskarnan d'inke, yasha rawani abin zak'k'yau kamar nabama (gwaurayen group d'ina shi🥴⛹🏻‍♀). Gefensa mom ta zaunar dani, tunda aka shigi wajen dani suka d'auki tafi, fuskata a rufe take, ba kallon kowa nakeba, saima hawaye dake cigaba da zirara har yanzun. Mom tad'an ja hancin Galadima ya murmusa, sannan takamo hannuna tasaka cikin nashi tabar wajen. K'amshin turarena da nasa ya had'e yabada wani kalar k'amshin Na musamman. Dukda kukana a hankali nakeyi mara sauti hakan bai hanashi jin ajiyar zuciyar danake saukewa ba, yad'an matsa hannuna dake cikin nasa amma baiyi magana ba, nima sai bance komaiba nacigaba da kukana. An fara gudanar da addu'oin fatan alkairi da zaman lafiya agaremu, sannan akamin barka da zuwa cikin wannan masarauta mai d'unbin tarihi, Mom takar6a tayi jawabi irina uwar kwarai mai tarin mutunci da kamala. aka shiga tafa mata, saboda taburge kowa. Hakama aunty Mimi tayi jawabi mai birgewa, sannan mama Fulani tafito cikin tsantsar izzarta da k'asaita tayi welcoming d'ina a wannan family, hakama matan Sarki, saikuma k'annen galadima mata da yayunsa, yayun momma da k'annenta, komai yana tafiyane cikin nutsuwa, nidai ba ganin kowa nakeba, amma ina sarrarensu, har lokacin kuma hannuna yana cikin Na Galadima, yakan d'an murzashi time to time. Duk Na k'agara a tashi wlhy, dan jikina yayi masifar zafi saboda zazza6i, shikansa Galadima yanajin zafin a hannuna, ganin kamarma ina rawar sanyi saiya kwantoni jikinsa. Ban musaba, saboda babu abinda nake buk'ata a lokacin kamar kwanciya, ga barci ga ciwo da gajiya. Bayan angama jawabai da k'yaututtuka da kowa kan bani wad'anda aketa zuwa ana jibgewa a gabanmu aka fara gudanar da liyafar cin abinci kamar yanda komai yake a tsari, sai abinda kakeso za'a kawo maka. Muma ankawo fruits salad da gasashen kaza da snacks sai drinks da wani abinci dabansan miyeba an ajiye agabanmu. Da hannu Galadima yayi kiran aunty Mimi, ta k'araso inda muke. “my k'ani lafiya dai? Ko abincin bai matabane?”. “no aunty bama abinci baneba, batada lafiya fa, ta6a jikinta kiji”. Hannu aunty Mimi tasaka a wuyana, tausayi nabata saboda zafin da jikina ya d'auka, “to yaza'ayi yanzu? ko tad'an k'ara hak'uri kad'an tunda naga ankusa tashi, kasan halin mama Fulani, kuna tashi yanzu zata d'aukeshi wani Abu daban, dama wannan d'an kwantar da itan dakayi ajikinka inaji tana maganar bakada kunya wai”. Guntun tsaki yaja yace “canta matse mata, indan tagadama tacika masarautarnan da surutu, nanda minti 30 inba'a gamaba zamu tashi kawai”. “karka damu zama'a gama insha ALLAH”. duk maganar dasukeyi ina jinsu, sai naji tausayin kaina ya kamani, domin nafahimci nanma akwai mai irin halin innaro kenan. Wasu hawaye suka silalomin a kumatu, sauk'i nama auren 1year ne Na kama gabana. Daga ni har shi babu Wanda yaci wani Abu har aka tashi a taron, lokacin 12pm, yanzuma mom ce takama hannuna muka koma 6angaren da aka fara kaini, muna shiga kwanciya nayi, bayan mom tasakani cire alk'yabbar jikina, duk kunya ta rufeni, ganin haka yasata ajiyemin kayan barci masu kauri ta fita, a hanzarce na shirya na saka hijjab sannan na kwanta, saida ta kintaci time sannan suka shigo itada aunty Mimi da Galadima sai wani ba'indiye, Ashe abokinsa ne dayazo biki, kuma doctor ne. Galadima ya zauna a bakin gadon kusada kaina, dayake na juya musu bayane, bargon Dana rufa har fuskata yad'an janye, Idan Akash yay tambaya saishi ya d'an rankwafo Dan yaji amsar da zan bada, saiya maimaita masa abinda na fad'a. Bayan gama tambayoyin Akash yace damuwa ce da gajiya kawai, ya rubuta maganin daza'a sayo min, (duk cikin harshen ingilishi suke maganar). Kar6a Galadima yayi ya d'auki waya yakira Harun, sunan maganin ya Sanar masa sannan ya yanke wayar, mintuna 10 saiga Samha takawo maganin. Ya kalli mom yace, “amma bataci abinciba ai”. Kallon Samha mom yayi, tace “taje ta had'o min tea. Samha na kawowa duk sai suka fice suka barni dagani sai shi, shima Akash fita yayi. Bargon jikina ya yaye gaba d'aya, muryarsa a dake yace “tashi kisha”. Shiru na masa, hakkane yasakashi kausasa muryarsa, “wai bak'ya jinane?”. Yun k'urawa nayi na tashi da k'yar, kad'an na saci kallonsa, harya cice kayansa na d'azu, yana sanye da dogon bak'in wando da T-shirt mai gajeren hannu, gefen wandon anmasa zane layi 2 da farin zare. fuskarshi babu walwala kamar kulum. Mug d'in tea n ya mik'omin bayan na gyara zamana na jingina da gado, ALLAH ma ya soni sanye nake da hijjab. Kar6a nayi dan nima nasan harda yunwa ke cina, inaga rabona dawani abincin kirki tun ana jibi d'aurin aurenmu, (ranar kamu). Nasha rabin cup d'in na mik'a masa, bai kar6aba yashiga hararata, cikeda k'asaitarsa yace “cup d'in kawai nake buk'atar gani, kina 6atamin lokaci zanje na kwantane”. Tamkar na makeshi haka naji, na harareshi nima a k'asan ido, muryata na rawa nace “wlhy na k'oshi, zanyi amaine”. Bai tanka minba kuma bai k'ar6i mug d'inba, hakan ya nunamin dole dai saina shaye kenan, haka na rumtse idanu na shanye na mik'a masa mug d'in. Kar6a yayi ya ajiye saman table glass d'in dake gabansa, sannan yad'auki magungunan ya 6alla min, bana tsoron Magani sai allura, dan haka babu musu na kar6a nasha tareda ruwan daya bani a cup. Ina gamawa na zame na kwanta, mik'ewa yayi yaja bargon ya lullu6a min sannan ya fice batareda ya tanka minba. Babu dad'ewa barci ya kwasheni, bamma San su Ayusher sun shigo sun kwantaba suma. da yake gadon babbane duk sai ya d'aukemu. Washe gari natashi dad'an sauk'i, sai dai kewar munubiya data innarmu, harma data gayyar tsiyar 'yan gidanmu, sauk'i nama d'aya ina ganin su Feena. Break fast mai rai da lafiya aka kawo mana, su Ameera sai zuba santi sukeyi, nidai uffan bance da suba, nad'an tsakura kad'an na turo, maganin jiya na d'auka nasha na safe, dan har lokacin kaina na ciwo kad'an-kad'an, babu dad'ewa barci yay awon gaba dani. Ban farkaba sai 12, shima tadani akayi, wai za'ayi ko hawan mi, nidai wannan bidi'a ta isheni hakanan wlhy. Shiri akamin yanzuma cikin farin less, sanan aka samin alk'yabba, yanzun ma fuskar tawa a rufe take. Gaskiya gidan sarauta akwai girma, dan shimafa dole akirasa da suna wani gari guda kam. A mota aka sakamu zuwa inda za'a gudanar da hawan, dukda kuwa acikin gidanne fa, nida Samha ne kawai a mortar, tana ta zubamin surutu har muka isa. Wata daban santa bace ta fitar dani daga motar, tana rik'e da hannuna har gurin da aka tanada domin zamana, yanzun fuskata a bud'e take, ba'a sakamin hular alk'yabba d'inba, dan muna zama awajen matar data fidoni ta ciremin, sai dai kunya tasani kasa kallon kowa, duk tsiwata inada tsananin kunya da rashin son zama wajen da mutane suka cika yawa. Aunty Mimi ce a gefena na haggu. Ban iya kallonba saida ta min magana tana kamo hannuna, dole babu yanda na iya na kallesu, su Galadima ne a saman dokuna shida samari kusan biyar duk da irin shigarsa ta sarauta, dokunan suna a tsaitsaye, da alama umarni suke jiran abasu, dan kamar gasace zasuyi. Caraf muka had'a ido dashi, murmushin gefen baki ya sakarmin, cikeda mamaki na janye idona daga kallonsa. Ana busa wani k'aho kowa yabama dokinsa k'aimi suka rera da gudu, nanfa hankalin kowa yakoma kansu ana zufa tafi, babu wata hayaniya dan bawani yawane damuba, kusan ma wajen duk 'yan matane sai abokan Galadima dasuke son ganin al'adar dabasu saniba. Saikuma yayunsa mata irinsu aunty Mimi, amma babu manya kamar su mom awajen. Ni ban saniba Ashe wannan tafiya saisun zagaye masarautar su dawo, Wanda yafara zuwa shine na d'aya. Muna nan kusan mintuna 30 saigasu aguje suna tada k'ura, ko ganin fuskarsu ma ba'ayi sosai bare kagane wanene a gaba. Jinai kawai ansaki tafi kowa na ambatar Galadima! Galadima!!, wai Ashe shine yafara isowa. ya diro akan dokin yana murmushi da goge hannunasa da handkerchief d'insa daya zaro aljihu, sannan yagoge fuskarsa. Ruwa wani dogari ya mik'a masa, ya d'auka daga saman tired'in da aka d'oro yabud'e Goran, batareda ya saka kofiba ya hau shan kayansa, tas ya shanye ya jefar da robar, suma sauran duk ruwan suke sha. Daga nan hotuna akayi, sannan yazo har inda muke ya kama hannuna, wai Ashe nima yanzu dole saina hau dokin, ahakane zamuje sashe-sashe, dan kowa yanacan yafito waje yana jiran zuwanmu. Banta6a hawa dokiba sai yau, dan haka jikina yakama rawa. Muryarsa can k'asan mak'oshi yace “k bak'auya ki nutsu”. Maganarsa saida tabani haushi amma ya zanyi, da taimakonsa na hau dokin bayan dogarai sun baza rigunansu yanda baza'a ga hawa naba. Saida na hau da k'yau sannan shima yaje ya hau nasa, kuyangine a gabanmu suna zuba flowers, a bayanmu kuma dogarai, gefe da gefenmu ma dogaraine, wasu suna busa algaita wasu suna kid'an taushi, sai gayyar abokansa biye damu abaya dasu Ayusher da 'yammatan masarautar. Ahaka muka dinga zuwa sashe -sashe inda duk sun firfito, duk muna akan dokin bamu saukaba, sai dai mukan risina alamar gaisuwa. fuskata kuma tana abud'e yanzun kowa Na ganina, saida muka zagaye ko ina a masarautar sannan aka maidani wajensu mom. Lokacin la'asar tayi. Dukna damu saboda kiran munubiya danaketa yi wayar akashe, tsakin danakeyine ya saka Ayusher tambayata, na fad'a mata. Dariya tayi, “yo banda abunki ina zakiji munubiya kuwa, yaa marwan nacan nashan amarci kema kin sani ai, kema zuwa gobe wazai kiraki ya samu, Galadima nacan yana kwa.....”. Filo na d'auka Na jefa mata a fusaka, suka sanyamin dariya kuwa. ★★★★ Nasha kuka yayin tafiyarsu Ayusher, inaji ina gani suka tafi suka barni nikad'ai cikin wad'anda ban saniba. Tun magriba aka shiryani tsaf cikin wata tattausar atanfa, sannan aka d'oramin alk'yabba, wlhy nagaji da saka alk'yabba r nan, saboda nauyi sukemin, har mamaki nakeyi yanda su basu damuba. Zan iya cemuku nidai yau wanka akamin da turare dan kowane lungu da sak'o na jikina saida yasha ruwan turare, ruwan danayi wanka dashi kansa na musamman ne, nayi k'yau harna gaji. An fiddoni aka sakani cikin mota, sannan aka nufi sashen Galadima dani. Dukda nasan auren Contract nayi, hakan bai hana zuciyata luguden dakaba, tunda bamuyi wata yarjejeniya dashiba ta zaman da zamuyi, addu'a natayi a zuciyata ina tunano innarmu da munubiyata da kewarta ta gallabeni, jinake tamkar mun shekara 5 bamuga junaba, bamu ta6a yini ba'a tareba, saigashi yau munyi kwana da yinima, ko'a waya bamuji muryar junaba. Duk da fuskata a rufe take hakan bai hanani shaida 6angaren Galadima ya had'uba, dan k'amshinsa ma da banne. Muryar wata na tsinkayo a cikinsu tana fad'in wai falon Galadima za'a kaini, gabana yakuma fad'uwa. Nidai naji mun iso inda turaren Galadima yafi ko ina yawa, inaga nanne falon nasa, gawani lallausan Abu danake takawa a k'afata, sun zaunar dani akan wani laushin dayafi Wanda nake takawar, sannan sukayi addu'a suka fice. Tunda suka fita ban iya d'ago kainaba, dukda falon tsitt yake alamar babu kowa cikinsa, sai k'arar AC kawai da ni'im taccen k'amshin dake tashi, a falon, sai TV dake magana can k'asa an rage k'arar sosai, hawayen danaketa rik'ewa tun d'azun suka shiga ziraro min a kumatu. a hankali nakejin takun takalmi na tunkaro falon.........✍🏼 Muhad'u tomorrow idan munkai da rai da lafiya, yau kaina namin ciyo kuyi manage da wannan please🤦🏻‍♀. Ko Galadima zai angwance oho mar😜🥳. ⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu👏🏻😭_* *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣2⃣ ..........Takun takalminsa yana bada sautine dai-dai da kowacce dak'ik'a na bugawar zuciyata, gaba d'aya saina nemi jarumtata na rasa, musamman da firarsu a Ayusher tashiga dawomin a zuciya. Zuciyata tashiga tsitstsinkewa, saikace ba Munaya mai tsiwarnan ba da rashin barin kota kwana, kululu cikina yabada sauti lokacin da aka murd'a handle d'in k'ofar. kamshinsa ne ya buso min har cikin hancina. Shikam cak yatsaya yana kallona da mamaki, yasan wannan aikin aunty Mimi ne ko mom, yakuma tamke face saboda tsaro ba tsoroba😎. Oho ni bamma san yanayiba, nima tawa ta isheni a zuciya, dan wani tsoronsa ALLAH ya dasamin lokaci d'aya. kusan mintuna 2 yana a tsaye tamkar bak'on falon, yayinda k'amshin turarena ke dukan hancinsa, yau da ace auren soyayya yayi da wadda yakeso, babu abinda zai hanasa sauke nauyin daya damesa tsawon shekaru. a hankali yacigaba da takowa har cikin falon, ya zauna a kujera mai zaman mutum biyu cikeda izza, k'afarsa d'aya a kan d'aya yana wani kallona a k'asan idanu, shiru kakeji tamkar bama a cikin falon....... Muryata a sanyaye nace “ina yini”. tamkar bazai amsaba, saikuma yace “lafiya”. Daga nan kowa yay shiru. Knocking d'in k'ofar da akayine yasakashi sauke 6oyayyar ajiyar zuciya, cikin muryarsa mai kama da anmasa dole ya tambayi wanene?. Cikeda girmamawa sarkin k'ofar yace, “nime ranka ya dad'e, dama an kawo sak'one”. Kansa ya jingina da kujera, sannan yace “su shigo”. Kuyangi kusan biyarne suka shiga falon da sallama, duk muka amsa akan la66a, suka dire kayan hannunsu sannan suka zube suna kwasar gaisuwa agaremu, hannu kawai ya d'aga musu, nidai koma motsi banyiba, dan nima kunyama nakeji idan naga sun durk'usa suna gaidani, danfa wasuma sun girmeni sosai wlhy, wasuma sun haifeni, kai sarauta dabance gaskiya, al'amuransu sunada wahalar gaske, nidai harma yanzu ban fahim ci komaiba wlhy. Bayan fitarsu da kusan mintuna 4 naji alamar mik'ewarsa, yanzu ma baice dani uffan ba yashige wani d'aki danake k'yautata zaton bedroom d'in sane a wajen. Guntun tsaki naja, a raina nace ALLAH ka rabamu da girman kai dai wlhy. Ban damu da cire hular alk'yabba d'inba, dan sanyin Ac yasa ban takura ba, sai zamana dana gyara sosai yanda zanji dad'i da k'yau a saman lallausar kujerar, duk da har yanzun a tsoracen nake kuwa. dan wannan d'an jinkan yafi k'arfina, zai iya amfani da k'arfinsa ya cutamin batareda yayi la'akari da matsayin auren namuba. Shikam yana shiga d'akin nasa yafara k'ok'arin cire bottom d'in rigarsa, idon sane ya sauka akan gadonsa dake lailaye da zanin gado blue, dan komai nasa na nan white and blue ne, sa6anin na India dasuke White and Golden, kuma matsawa yayi sosai saboda ganin farin k'yalle dake saman bedsheets d'in. Tsaki yaja yana fad'in “waisu wad'annan mi suke nufi da shinfid'amin wannan farin abun a saman gado? samazo su d'auki kayansu yanda suka ajiye, motsww”. Yakuma jan tsaki sannan ya shige bathroom. Acanma yana wankan yana jera tagwayen tsoki, bai wani dad'eba yafito sanye da bathrobe milk, hannunsa rik'eda k'aramin towel yana goge fuskarsa zuwa kansa. Bai shafa maiba, wando yasaka da t-shirt duk milk color marasa nauyi, da alama yayi shirin barci kenan, ya d'auki turarensa na barci mai sanyin k'amshin ya faffeshe jikinsa, sannan ya saka silifas bak'ak'e a k'afarsa yakuma fitowa.. Kallona yayi da mamaki ganin ko fuskarta na kasa bud'ewa, ya ta6e baki da cije lips nashi saman ya zauna bisa tattausan carpet d'in tsakkiyar falon inda kuyangin suka ajiye kayan d'azun. Tankwashe kafafunsa yayi yashiga bud'e kwanikan domin duba abinda ke ciki. “halan kekam bak'ya jin zafi?”. Yayi maganar yana zuba fruits salad a k'aramin bowl na tangaran mai k'yau. Shiru nayi tamkar ban jishiba, shima saiya shareni yaja bowl d'in gabansa yafara sha a hankali tamkar bayaso. Duk abinda yakeyi ina kallonsa ta k'asan ido, saboda kaina Dana jingina da kujera. Kusan mintuna 5 yana shan fruits salad d'in tamkar wani k'aramin yaro, dan ko Rabin Wanda yazuba baiyiba, araina nace abincinma sai an masa sarauta kenan. Idanunsa ya d'ago yana kallona, “k wai bakijin ana Miki maganane? bazaki bud'e face nakiba?”. Saida naja kusan seconds 20 sannan na janye hular alk'yabba d'in. Janye idonsa yayi yacigaba da shan kayansa, nikuwa saima na zame na kwanta a kujera, dama 3setter ce, idanuna na maida na lumshe saboda ciwon da kaina yakeyi kad'an-kad'an, ga kewar innarmu da munubiya dasu Aryaan na damuna, ga wannan auren na fargaba na addabar zuciyata. Dukda yaga kwanciyar danayi bai tankaba, ya kammala shan fruits salad d'in yamik'e, saman kujera yakoma ya zauna, ya d'auki wayarsa yana latsawa, saikuma ya ajiye ya d'auki remote ya canja tasha zuwa labarai. Haka muka zauna tamkar kurame, shi yana kallon labarai yayinda nikuma barci 6arawo ya saceni batareda na shirya ba, to gajiya na nuk'urk'usata. Shi duk bai farga barci nakeba harya kammala kallon labaransa ya kashe tvn, kallona yayi da nufin min magana saiyaga kamarma nayi barci a haka. Yay d'an jim yana tunanin tayaya zai tasheni, danshi soyake ya shige yayi shafa'i da wutiri ya kwanta, a ganinsa kuma bai kamata ya barni a wajenba. Matsowa yayi kusada kujerar, ya d'an bubbuga hannun kujerar, dama barcin nawa baiyi nisaba, na bud'e idanuna dasukayi d'an jaa a hankali, saboda barcin dana fara. “tashi muje ki kwanta”. Gabana ya fad'i, amma saina yunk'ura da k'yar natashi zaune. Ganin ya nufi k'ofar futa sainaji d'an sanyi, tashi nayi nabi bayansa muka fita, bakowa falon alamun duk suntafi makwanci. Wani falon muka shiga daban kuma, gaskiya shima ya had'u, komai na cikinsa lemon green ne da milk, sai tashin k'amshin turaren wuta da air fresheners masu dad'i yake. bai tsaya ananba yay gaba, nidai ina binsa abaya kawai, munshiga k'aton bedroom tamkar nasa, saidaifa aganina nasan yafi had'uwa duk da ban ganiba, nanma komai lemon green ne acikinsa, sai labuloli milk kamar falon, shima yanata tashin k'amshin. Juyowa yayi ya kalleni “nan shine d'akinki”. ‘yayi maganar tamkar an masa tilas’. Uffan bance masaba, sai d'aga masa kai nayi alamar naji, shima bai sake cewa komaiba ya fice abinsa. d'akin na shiga bi da kallo, yamin k'yau sosai, na cire alk'yabba jikina ina sauke numfashi, sanan na cire sark'a da 'yankunne da bangles d'in duk na zube saman madubi. Suma kayan na hau cirewa dan bazan iya barci da suba, sai kuma na shiga tunanin inda zan samu kayan barci? tunda lefena suna gidanmu ba'a kawoba, akwatin da'a kawoni dashi kuma jiya ban Ganshi a d'akinba, zuciyatace tabani shawarar duba wardrobe d'in dake d'akin, banyi musuba naje na bud'e, a mamakina saina ganta da kaya, sai dai duk k'ananune, kayan barcinma babu na mutunci, tamkar zan fasa kuka haka naji, da k'yar nasamu wasu Riga da wando masu sauk'in fidda tsiraici, duk da suma d'in dai sai a slow. Gadon na hau amma saina kasa barci, kewar 'Yar uwata yadawomin sabuwa, na tashi zaune na fashe da kuka. Ina zaune ina kukana sai kawai naga mutum yashigo min da sallama ciki-ciki. Da Sauri na jawo gyalen dana ajiye gefe na yafama jikina, plate d'in hannunsa ya ajiye a table d'in dake jikin gadon, dan harya kwanta yatuna banci komaiba, gani yayi bai dace ya barni da yunwa ba, danni bak'uwace yanzu a gidan, dole sai an bani zanci. Tamkar bazai tankaba saikuma ya kalleni, “mike faruwa kike kuka?”. Wasu kwallanne masu zafi suka sake kwararomin, na sharesu da gefen gyalena nace, “wlhy ni tsoro nakeji, ban ta6a kwana ni kad'aiba, dan ALLAH ka kiramin Samha ta tayani”. Shiru yay ya tsaya kawai yana kallona, azuciyarsa yace kajifa wannan yarinyar dawani batu, kawai saina tafi kiran Samha ta tayata kwana?. guntun tsoki yaja, Wanda yasakani d'agowa na kallesa. Ya cije lips d'insa sannan ya juyo yakuma kallona “mikike nufi da bazaki iya kwana ke kad'aiba? kin san dai babu wanda yasan manufar aurenmu, daga ni sai ke sai muftahu, dolene ki koya ma kanki iya kwana ke kad'ai d'in, sannan inason kisanfa dolene ki dinga canja behavior naki agaban mutane, domin su agaresu aurene mukayi kamar kowa, sannan ta wannan hanyarne kawai zamu iya samun wani avoidance a kan case d'inan, nasan kinada wayo dan haka saiki bud'e idanunki dan kema zaki iya zama security d'in kanki da kanki, game da zaman gidannan kam za'a samu mai koyar dake komai, dan komai a tsare yake, sauran bayani zamuyishi daga baya, kisa a ranki zaman da zamuyi dake zamane na taimakon juna irinna abota, bayan aiki ya kammala zan baki sakinki kamar yanda nayi alk'awari”. Duk da hawayen dake neman zubo mini haka na had'iyesu, cikin aro jarumta nace, “insha ALLAH komai zai tafi yanda yakamata, kuma zaka sameni mai tsare gaskiya da amana, ALLAH yabamu nasara, ina fata da lokaci yacika komai ya bayyana zaka cika alk'awarin sakina?”. Batare da ya kalleniba yace, “zaki sameni mai cike alk'awari insha ALLAH koda ace bamu cika shekararba komai ya bayyana zan sakeki, idan kuma ashekara 1 bamu samu yanda Muke soba zamuyi 2 ne kamar yanda nafad'a miki tun farko, amma inama addu'ar kafin shekara komai yazama done OK?, ga abinci nan kici, kiyi addu'a ki kwanta, zakiyi barci insha ALLAH”. Batareda ya jira cewata ba yay ficewarsa, kusan mintuna biyu idona na kallon k'ofar, saikace zanga dawowarsane, mamaki yabani sosai, dama yana magana mai yawa irin haka? Kuma cikin kwantar da murya. na sauke ajiyar zuciya tareda bud'e plate d'in daya ajiye, gasashen namane mai rai da lafiya, yawu nane ya tsinke, gashi dama inajin yunwa, na mik'e na bud'e fright d'in dana gani ad'akin, ruwane kawai aciki aka zuba, guda d'aya na d'auka na dawo saman gadon na zauna, inacin naman ina hawaye, gaba d'aya kewar 'yan uwana ta gallabeni, musamman Munubiya, waya na d'auka na kuma gwada kiranta, amma still akashe, wasu hawaye masu zafi suka kuma kwararowa a kumatuna, naman na ture gefe naciga da kukana, saida nayi mai isata sannan natashi nashiga toilet d'in d'akin na wanko fuskata da bakina na d'auro alwala, a fright d'in na saka naman da sauran ruwan na kwanta kamar yanda yabani shawara, addu'ar barci nayi sannan narufe ido. tunani yace salamu alaikum, haka naita juye-juye a gadon, barci 6arawo bai saceni ba sai around 3. daga nan ban sake sanin inda nakeba saida naji ana bubbuga gefen filon danake kwance. Da k'yar na bud'e idanuna dasuka kumbura saboda kuka da rashin isashen barci. Galadima ne tsaye a kaina, sanye cikin jallabiya ruwan hanta, tamasa k'yau dukda kallon fisha na masa. Agogon d'akin ya kalla sannan ya juya zai fita yana fad'in “kitashi kiyi salla”. Da k'yar na iya sauka, dan jikina duk ciwo yakemin, ga barci danake masifar ji. daurewa nayi nafara wanka da ruwa mai d'an zafi sannan nayo alwala nafito, salla na gabatar ta asuba nayi addu'oina sannan namik'e na koma gadon, dan danan barci ya kuma kwasheni. ★★★★★★★ A gidanmu bayan kwashemu dukkan amare washe gari 'yan biki suka fara kama gabansu, sai makusanta ne kawai aka bari. Lokacin da su Ayusher suka koma sun iske innaro na zuba tijara a tsakar gida, wai an munafunceta ba ace ta fitoba lokacin da akazo d'aukata, dama tasan innarmu bak'in ciki take mata karta dangwali arzik'i, to kuwa ita k'adangaren bakin tuluce, babu yanda aka iya da ita, duk wani makirci da innarmu zata shirya mana akan karmu taimaka mata dolene tanan matsayin uwar ubanmu. 'Yan gidanmu fa abin nema yasamu, saifa aka hau dariyar gatsa-gatsa suda sauran bak'in su. Innarmu kam murmushi kawai tayi, zuwa yanzun ita ta wuce k'aramar yarinya, dama sarai tasan bawai nadamar gaskiya innaro tayiba, kawai dai wani abu dake a ranta kawai. Ko lek'owa batayi tsakar gidanba, barema tanuna tasan da ita takeyi. Shigowar su Ayusher da kaya nik'i-nik'i na biki da mom tabasu yasa innaro waryar leda d'aya tana fad'in munafukai, Ashe kune aka tura domin Ku tattaro komai, to ALLAH ya fiku, kafin mai biri yaga mai gona mai gona yaga biri”. Ayusher zatayi magana mama Rabi'a ta hanata, haka suka shige da sauran kayan suna k'unk'uni. Innaro na bud'ewa taga duk drinks ne aciki saita biyo bayansu, ledar ta dangwarar a k'ofar falon tana kunfar baki, “bazansha kayan ruwan ba kayan fitsari, yanzu-yanzu a canjamin kokuma na kwashe komai babu yanda za ayi dani dangin tsiya dangin rashin asali, kai ALLAH yarabamu da bak'ar zuciya mai cike da nunkufurci dai wlhy”. Babu wanda ya tanka mata, Mama Rabi'a ta bud'e komai ta d'iba mata, tanuna ledar datafi kowacce girma da mama Rabi'a bata bud'eba, “to uwar iya, ita waccan ledar miye aciki?”. Da sauri Bilkeesu ta d'auke tana murgud'a baki, “wlhy babu mai baki wannan, domin a lissafe suke, kuma mu aka bamawa bawaniba, zannuwane”. “to 'Yar karoro, kekuma asuwa gand'oki muje biki? Aiba uban wani ya Haifa min Auwalun ba daya haifi munaya, saiki bari sai ALLAH yabaki farin jinin auren koda kansilan anguwarkune sannan kimana iyayi, kujimin bak'ar banza kawai”. Baki Bilkeesu ta ta6e, suka ja ledar itada feena suka shige tsohon d'akinmu, yayinda su Ayusher da Ameera suka take musu baya. Daga mama Rabi'a har innarmu babu wanda ya dakatar dasu. Aiko sai innaro ta saka kuka wai su Ayusher sun zageta agaban innarmu batace komaiba. Duk abinda ke faruwa 'yan gidanmu na tsaye cirko-cirko suna dariya. Yaa Hameed daya shigo gidanne yazo har inda innaro ke tsaye a k'ofar fallon innarmu yana tambayarta lafiya?. Cikin kuka da shar6e majina ta kora masa bayani, Kansa kawai ya girgiza, danshi lamarin innaro baya burgesa. Da lallashinsa tahak'ura tafita yarakata har gidanta da ledar da mama Rabi'a ta zuba mata kayan bikin. Acanma zage-zage taitayi tana aibanta innarmu, kunya dukta ishi gwaggo Safiyya ga sauran 'yan biki suna saurarenta, gwaggo Safiyya fitowa tayi ta baro gidan, gidanmu tashigo tazo tana bama innarmu hak'uri. Murmushi innarmu tayi, tace, “wlhy babu komai gwaggonsu, ai inna nima mahaifiya tace, mizaisa dantamin Abu yazama ya 6atamin rai, ai ta Isa danine shiyyasa”. Innarmu ta bama gwaggo Safiyya tausayi, tana k'ara jinjina hak'urin innarmu a ranta, tabbas da acikin sauran matan gidanne da innaro ta magantu, dan ba raga mata zasuyiba, danma suna Shankar mazajen gidan su Abbanmu. ★★★★**•°•°•°•**★★★★ Su Munubiya amaryar yaa marwan, 🙊baiwar ALLAH taban tausayi, dan kallo d'aya namata nasan yaa Marwan ya ajiye muskilamci ya kashe arna😎. Duk takuma zama wata silent, tana kwance a falonta dayayi k'yau da tsari, hannunta dafe da kanta, idonta arufe tamkar nai barci, tunanin innarsu da kewar 'Yar uwarta ya gallabeta, gashi tun shekaran jiya yaa Marwan ya kar6e phone nata ya kashe, tayi rok'on duniya yabata takira Munaya da innarsu amma k'ememe ya hana, yadai kira mata innar sun gaisa jiya da daddare, amma munaya yace ba yanzun ba. hawayene suka ziraro ta gefen idonta. Tun d'azun yashigo yake kanta tsaye bata saniba, tsigunnawa yayi saitin fuskarta yafara share mata hawayen, da sauri ta bud'e idonta, ganinsa yasata tashi zaune tana k'ak'aro murmushi damasa sannu da zuwa. Bai amsaba, sai zama dayayi kusada ita yajawota jikinsa ya rungume, “haba my baby yanzu kukannan bazai k'areba? ko har yanzu wajen yana ciwonne nasake had'a miki ruwan zafin ki shiga?”. Kanta ta girgiza masa tana kuma matso hawaye, murya na rawa tace “ina kewar Munaya”. Tausayi ta bashi, tareda mamakin tsantsar k'aunar da sukema juna itada 'Yar uwar tagwaicinta, shikuma wlhy bayason kiran Munayar ne saboda karsu shiga hak'in Galadima, amma yanzu kam bashida mafita, yakai dubansa ga agogon falon, 11:49am, maybe zuwa yanzu sun tashi, wayarsa ya d'auka ya lalubo number Munaya yafara kira. cikin sa'a kuwa sai gata tashiga. Mik'ama Munubiya yayi, cike da d'oki ta kar6a tana murmushi tana hawaye, shi saima abin yaso bashi dariya. Ina cikin barci naji ringin d'in wayata, da k'yar na lalubota batareda na dubaba nayi picking kawai, a kunne na kara cikin muryar barci nayi sallama. Daga can Munubiya ta amsa mani. Ai zumbur namik'e zaune danjin muryar gudan jinina, “Sweetheart kece? Wlhy I Miss u so much ”. ‘nafad'a ina share hawayen dasuka ziraromin’. Itama Munubiya hawayen takeyi, muryarta na zuga tace “miss u 2 sweetheart, I love you I love you for ever”. sai kawai ta rushe da kuka tareda fad'awa jikin yaa Marwan dake kallonta tana rera kukanta. Hannu yasaka yana bubbuga bayanta yana murmushi, yayinda nima naketa maimaita mata kalmar I love you ina kuka. Wayar yaa marwan ya kar6a, muryarsa kawai naji yana fad'in “to kukan ya Isa haka kema, kar Galadima yagani ya d'auka munyi miki wani abune, sai anjima idan kin nutsu masake kiranki”. d'if ya yanke, batareda yajira amsa taba. Sai kawai nakuma ruahewa da kuka na fad'a saman filoluwan da suke zube a saman gadon. Galadima dake tsaye bakin k'ofar yazo dubani saboda dangin mom da zasuzo mana sallama, saiya koma da baya bai bari na gansaba, zuciyarsa tana masa tunanin dawa nake waya? har nake jera masa kalaman I love u?. Ya d'an ta6e bakinsa, tareda kauda tunanin a zuciyarsa, to shi inama ruwansa, kwana nawane zai bani takardata na kama gabana. Falonsa yakoma ya zauna yana jan tsakin Aiken mama Fulani na d'azun data tuna. Yakuma jan tsakin yana gyara zamansa, dolene ya takama tsohuwarnan birki da wuri, inba hakaba tana neman Shiga masa hanci. Abinda yafaru d'azunne da safe kusan around 7:30, yadawo daga masallaci bayan yaje ya tadani yadawo d'akinsa, zaune yake a doguwar kujera a falonsa yana azkar kamar yanda yasaba a kowacce Safiya ta duniya. sarkin k'ofane yamasa knocking. “waye?” yayi tambayar batareda ya bud'e idanunsa dasuke a rufe ba. Sarkin k'ofar ya amsa da “nine ranka ya dad'e, dama Amintacciyar kuyangar Fulani Ce ke Neman iso”. Saida yaja guntun tsuka sannan yace tashigo. Babu dad'ewa saigata kuwa, saida tayi sallama a k'ofar yabata izinin Shiga sannan ta shigo, risinawa tayi (dan ya hanata durk'usa masa saboda ta manyanta sosai) tana fad'in “barka da Safiya ranka ya dad'e”. Idonsa yabud'e a kanta yace “kin tashi lafiya”. “lafiya lau ranka ya dad'e, dama Fulani ce tace azo a d'auki yankin jiya”. Bai fahimceta ba, dan haka yace “miyene hakan?”. “ka gafarceni ranka ya dad'e, yankin farin k'yallen mutuntaka da aka shinfid'a a gadonka jiya”. Bakinsa ya ta6e, ya maida kansa ya jingina tareda maida idonsa yanda suke, kusan minti 1 harma ta fidda ran zai amsa, saitaji yace “kije kawai, zan kawo mata da kaina”. Idanu tad'an zaro waje saboda mamakin zancensa, amma babu yanda ta iya, kowa a masarautar yasan murd'ad'd'en hali irinna Galadima, saidai akwaishi da kirki da yawan k'yauta. ta risinar da kai, “na barka lafiya ranka ya dad'e, afito lafiya”. Uffan baice mataba harta fice tarufo k'ofar. Azkar d'insa yacigaba dayi batareda ya maida hankaliba. Mom ce takirasa a waya, bayan ya gaidata cikin mutunci ta sanar masa gasunan zuwa sashensa suyi sallama, dan jirgin 1pm zasubi ya maidasu tasu masarauta. Wannan dalilinne yasakashi zuwa Sanar min, amma saiya Tatar ina Waya da fad'in I love you ina kuka kuma, shine yajuya batareda yayi maganaba. Kamar na sani natashi na gyara gadon fes, nad'anyi shara dukda babu wani datti, toilet nashige nayo wanka. Ina tsaka da shiri najiwo sallamar da wata murya ketayi tun d'azun, a gurguje na shirya naje na bud'e k'ofar. Yarane matasa a durk'ushe can gefe a falona, sai wad'anda suka d'an girme musu su biyu. Ina fitowa suka zube suna gaidani, abinda baka saba ganiba to, duk sai kunya ta kamani, nace “please Ku tashi minene ya faru?”. “d'aya acikinsu tace “ gimbiya ranki ya dad'e, ki gafarcemu mune masu miki hidima. ni sunana Alawiyya nice mai gyara miki makwancinki kawai da shiryaki, sukuma wad'annan zasu cigaba da sauran hidimominki, irinsu gyaran falo, girki, wanki, baki labari, da sauransu”. Babbar jaka uba, shirinma sai anmin kamar wata 'Yar baby, nidai naga idi gaskiya, wannan wace iriyar rayuwacw haka?. “ranki ya dad'a zamu iya fara aikinmu?”. Alawuyya takuma maimaitawa a aladabce. Kafin nabata amsa muka jiyo gyaran murya a abayanmu. dandanan naga sun juya suna kwasar gaisuwa, jikinsu har 6ari yakeyi. Hannu kawai ya d'aga musu, kafin yabud'e baki da k'yar yace, “miya faru ne?”. Alawuyya takuma rissinar dakai tace, “ranka ya dad'e mune masuma gimbiya hidima”. Shiru tamkar bazai amsaba, yad'an yamutsa fusaka yana gyara tsayuwa “wanene ya turoku?”. “ranka ya dad'e mama fulani ne”. Baice komaiba ya ra6a ta gefena zai wuce ciki, harya kusa shiga sannan yace, “zaku iya tafiya zan nemeku”. Atare suke fad'in godiya muke ranka yadad'e, ALLAH ya kiyayeka, yatsare bayanka da gabanka. To tunima yariga yashige, nikam tausayi suke bani wannan abun dasukeyi, nace “please kutashi kuje kawai”. “to ranki ya dad'e, godiya mukeyi........ Nidai juyawa nayi nashiga d'akin nima, dan banason wannan kirarin wlhy.................✍🏼 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*👏🏻😭 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _____________________________ _Wannan page d'in na sadaukar dashi agareki Hafsat writer d'in *HAFEEZ* na gode sosai, ALLAH yabar zuminci, Bilyn Abdull na yinki irin sosai d'inan dear🥰🥰🤝🏻❤._ ______________________________ 👉🏻2⃣3⃣ ..............A saman sofa na iskeshi zaune, ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana waya. Idanu ya d'ago yad'an kalleni ya janye. kunyace takamani saboda babu ko gyale ajikina, gashi kayan sket da rigane, kamar munafuka haka nawuce inda akwatina yake da aka kawo da safe, nima farkawa nayi kawai na gansa a d'akin. Gyale na d'auka na yafa, sannan naje bakin gadon na zauna ina sauraren wayar dayakeyi, abinda na fara lura da halayensa shine, shi mutumne marason hayaniya, komai nasa zaka sameshi a nutse yakeyi, yanzu haka a d'aki d'aya muke zaune, amma ba komai nakeji ba a maganar dayakeyi, ga jan aji tamkar wani mace, jinin mulki dake yawo a jikinsa ne ke k'ara masa k'asaita da izza....... Gyaran muryar da yayce yasakani d'agowa na kalleshi, idonsa a kaina, Dan haka muka had'a idanu, kowa janye nasa yayi cikeda basarwa. Saina samu kaina da cemasa “ina kwana”. Saida yaja wasu seconds sannan yace, “kin tashi lafiya?”. “Alhmdllh” kawai nace masa nayi shiru. Shiru mukayi babu Wanda yasake magana, yanata aikin latsa wayarsa, nikam ina satar kallonsa da mamakin wannan halayya tashi, shi koma takura bayayi? ina dad'i dan ALLAH kai kenan kullum baki 6am🤐. Kusan mintuna 5 muna a haka, bakajin komai a d'akin sai k'arar AC, ni dukma sanyin ya isheni. batareda ya d'agoba yace “mikike buk'ata akawo miki break fast?”. ALLAH shi k'yauta, nafad'a a raina kafin nace, “ko miyema”. Idanunsa ya d'ago yana kallona, baice komaiba ya janye ya mada ga wayar. sai kuma yasaka a kunne, “mom ki basu su kawo abincin ta tashi”. Bansan mitace masaba daga can, naga dai yayi murmushin gefen baki tareda yanke wayar. Ya kalleni yana gyara zamansa, tareda kuma shan mur alamun maganar da zaiyi important ce, “ki kimtsa su mom zasu iya shigowa a kowanne time, dan zuwa anjima zasu tafi, duk yanda dai zaki nuna musu wani Abu yashiga tsakanina dake kiyi, dan banason su tafi dawani zargi a ransu OK?”. Duk da na fahimci inda zancensa ya dosa, hakan bai hanani yimasa kallo mamakiba, nace, “kamar ya ban ganeba fa ni”. Shima kallon mamakin yamin, kamar zaiyi magana saiya fasa kuma, yad'an furzo huci a bakinsa kafin ya cije lips nashi da d'an k'arfi. tsaye yamike yana zuba wayoyinsa cikin aljihun ash d'in wandonsa, sannan yafara tafiya, sai da yakusan fita sannan yace, “ki nuna musu tamkar wata mu'amullar aure tashiga tsakaninmu, wannan shine kawai mafita, idan kin gama kizo kiyi breakfast”. ficewarsa ya ida yi. Yayinda nikuma na sauke ajiyar zuciya, danni maganganun nasa duk sunzomin a cirkud'e, to mom d'in nasa ba'a gidan takeba kome? Sannan kuma ai mu yakamata muje mu gaisheta bawai ita tazoba aganina, mi hakan ke nufi?. banida mai bani amsata, dan haka namik'e a gadon ina sauke numfashi, inason kiran Munubiya amma ina tsoron yaa marwan. wayar innarmu nakira, amma a kashe, idona yacika da k'walla, murya na rawa nace “wayyo innarmu I miss u wlhy”. jinake tamkar nayi tsintsuwa naganni a gida, dama ashe akwai randa zatazo na kwana Na tashi ba'a gidanmu tareda munubiya taba? gaskiya masu cewa aure da dad'i basuda kai wlhy, dan ALLAH ina wani dad'i anan?. Da Sauri Na goge hawayena saboda jin maganar Samha a kaina, jikinta a sanyaye ta zauna kusada ni, nima saina yunk'ura natashi zaune ina murmushi da share sauran hawayen fuskata. “Samha yaushe kika shigo”. Kanta ta langa6e gefe cikin damuwa tace, “Aunty yanzu na shigo, miya sakaki kuka? ko Uncle Sam.... ne?”. Murmushi namata, danni dariya wannan shagwa6ar tata ke bani, ko kad'an bata d'aukar kanta ta girma, “A'a Samha, ba shi baneba, ina kika shigene haka?”. “ina nan, tun d'azun naso zuwa Amma mummy ta hanani, yanzu ma tare muke dasu mom, suna falo kisaka Al'k'yabba muje”. Kallon jikina nayi, nace “bara dai na saka hijjab, ALLAH Alk'yabba d'inan nauyi takemin”. Dariya Samha tayi, “lallai aunty ai Indai kina gidannan dole saikin sakata, sai dai indan kun taho india, yanzu mafa dole ki saka”. Badan nasoba na d'akko Samha ta tayani sakawa, sannan muka fita bayan nafesa turarrurruka na masu dad'in k'amshi. A zatona suna falona, ashe suna nashi, Samha na rik'e da hannuna tamkar wata 'yar jagora har sashensa, Wanda sai yanzune nake d'an kallon wasu abubuwan, dukda face d'ina arufe take da hular alk'yabba. Sallama mukayi a k'ofar falon akabamu izinin shiga, gabana na dukan tara-tara muka shiga, duk zatona irin sunada yawa d'innanne, saina gansu su 5 kawai, kuma duk manyane, mom kawai na gane acikinsu, sauran ban sansuba, saikuma shi boss d'in yana zaune a kujerar mai zaman mutum d'aya kamar ma yana wayane. ban zauna akujera ba sai a k'asa, mom tayi saurin fad'in “a'a d'iyata tashi ki zauna saman kujera mana”. kaina na girgiza muryata a raunane nace “a'a nanma ya isa” sannan a ladabce na gaishesu. cikeda fara'a da sha'awa suka amsa, shi kansa uban gayyar saida ya kalleni, yaji dad'in girmamawar dana bama k'annen mahaifiyarsa. Samha ta gwargwad'ama mom magana a kunne, wai ta iskeni ina kuka. murmushi kawai mom tayi, tasan kukan bai wuce na shiga kwaryar manyaba, ga d'an nasu dagani jarumine (aikam mom ragone tunda ba abinda kike tunanin bane😜🤧). Kallon Galadima tayi dake harar Samha, “gulmammiya mikike fad'a? tashi kibar falon nan”. Tashi tayi tana tunzura baki, “wlhy Uncle Sam ni Vance wani abuba, Mom dan ALLAH wani Abu nace?”. Murmushi mom tayi, tace “a'a bakice komaiba”. Batareda ya kalleta ba yace, “naji, tunda kin rakosu wuce ki tafi”. Fita tayi tana daddaga k'afafu, yaja guntun tsuka, yayinda su mom suke mata dariya da tsokana irinta kakanni, nidai kaina na k'asa nima ina murmushin rigimar 'ya da Uba, duk dama har yanzu bansan yasukeba, naji dai tana Uncle kawai. Bayan fitar Samha d'aya acikin matan ta kalleni, d'iyarmu cire hular kisha iska kinji, mu nan duk iyayenki ne, daina jin kunyarmu. Babu yanda na iya, dole na zame hular Alk'yabba d'in, amma kaina na duk'e sosai yanda bazasuga fuskataba, nasiha mai ratsa jiki da 6argo suka Shiga mana daga ni har harshi, duk jikinmu sai yayi sanyi k'alau, nikam kukama nakeyi, Dan dama kad'an nake jira a ta6ani na fashe. sun dad'e sosai sannan suka ajiye min k'yaututtuka suka tafi harda shi domin musu rakkiya. Bayan fitarsu saina shiga rera sabon kuka, saida nayi mai isata sannan natashi da nufin tafiya nawa d'akin, kallon falon nashiga yi, masha ALLAH, komai yayi a falonnan, kujerun Navy blue ne, sai labuloli da Carpet sun kasance Silver da kwalliyar k'ananun flowers blue, babu wani tarkace sosai, wani hotonsa ne yay masifar d'aukar hankalina, gaskiya hoton ya d'auku, yana sanye cikin kayan sarauta akan dokin dashima yasha kwalliya, murmushin dake d'auke a face nashi shine Yakuma k'awata tsarin hoto, ga hoton irin k'aton nanne kamar kamasa magana ya amsa maka. Na juya na kalli d'ayan dake bangon kudu, shikam sanye yake cikin farin wando k'al da farar riga itama, ya tsuke k'ugunsa da bak'in belt, takalmansa da hularsa duk bak'ake, yana awani k'aton filine daya k'awatu da korayen ciyayi, hannunsa rik'e da wani k'arfe ga k'aramar boll a gabansa, nan ma fuskarsa washe da murmushi, har hakwaransa sun fito waje, a raina nace dama d'an wasan Golf🏌🏻 ne? kokuwa yasaka kayanne kawai?.🤔 Da sauri na juyo jin motsi a bayana, sai kunya ta kamani ganinsa tsaye hard'e da hannayensa a k'irji yana kallona, gudun karya zaci kallon hoton nake sainayi saurin cewa “dama kana buga Golf? ”. Murmushin gefen baki yayi, yatako a hankali ya zauna a kujerar dake kallon hoton, shima idonsa na kan hoton, ya d'ora k'afarsa d'aya kan d'aya.... Jin yayi shiru yasani juyowa na kalleshi, a tunanina kobai ji baneba, ido muka had'a, kowa ya janye cikeda basarwa, saiya lumshe nasa tareda jingina da kujerar, tamkar anmasa dole yace “kinason wasanne?”. Nace, “kusan haka, duk da bansan kan wasanba har yanzun”. Murmushi naga yayi kawai amma baice komaiba. Nima saiban sake cewa komanba na juya zan fita. idanu ya bud'e yabini da kallo harna fice. Yana mamakin yanda bata da tsoro, zai iya cewa itace yarinya ta farko budurwa dakan iya masa magana kanta tsaye bada wani shakkuba atare da ita. Tabbas a wannan fagen ya yaba mata, domin takafa tarihin da manyan 'yan mata masuji da mulki da Kansu suka kasayi, akwai 'ya'yan sarakuna da yawa dakesonsa amma sukan kasa fad'a masa, sunsha shan alwashi akansa amma da zarar sun had'u dashi sai alwashin nasu ya gudu, hakama 'ya'yan manyan attajirai, kuma baisan abinda yasa sukejin shakkar tasaba, shidai kawai abinda yasani baya sakar musu fuska, to ita wannan tatsitsiyar yarinyar koda fuskar tasa takai hadarin gabas murtukewa bata Shankar masa magana, ya cige lips nashi yana ta6e bakinsa wanda shiyasan dalilin yin hakan. ★★★★★★ Mama Fulani tagama cika tayi fam da rainin wayon Galadima, ba'a ta6a angon dayay abinda Galadima yayiba a masarautar, duk randa ango zai shiga d'akin amarya za'a kai farin k'yallen dasuke kira (yankin mutuntaka) a shinfid'a agado, washe gari za'a aika a d'ako domin kowa yaga mutuncin da yarinyar takawo, sannan dolene kuma kakawota da safe ta gaida matan Sarki da Sarki kafin yafita fada, saikuma sauran jama'ar gida wad'anda suka kasance iyaye. Amma saboda rashin mutuncin fand'ararren yaron can anje d'aukar k'yallen yace zai kawo da Kansu saboda shine shugaban marasa kunya na duniya, ta aika bayi masu hidima damata CID ya korosu wai zai nemesu, gashi ana neman k'arfe uku na yamma amma har yanzu baizo gaisuwa ba shida matarsa, sai bayintane ke sanar mata sunga yarako dangin uwarsa lokacin dazasu tafi, amma ita tunda yazi bikinnan bama ta sakashi a idonta ba sai ranar da akayi Mother's and tarbar amarya event ta gansa awajen. yaron nanfa yana shigar mata hanci da yawa fa, bari taga iya gudun ruwansa da k'arshen wutsiyar iskancinsa, ai ko ubansa bai Isa mata abinda gagararren yaronnan ke mata ba a gidannan. ★★★ Shi baima San tanayiba, Dan tun bayan fitar Munaya daga sashensa yatashi zuwa masallaci sallar azhur, ana idarwa ko yarda su had'u da Sarki baiyiba ya shiga gida, shigewarsa yay bedroom, yayi kwanciyarsa domin yasamu yad'an huta, jikinsa duk ciwo yake masa, saboda ainan-ainan na al'adar biki, dukda yasan ko Rabin hidimar da harun yayi shi baiyiba, saima ka rantse Harun shine angon wlhy. Bai wani dad'e da kwanciyar ba barci ya kwasheshi hankalinsa kwance. ★★★★ A gidanmu ma dai bak'i kowa yakama gabansa, an barsu daga su sai su, da daddare Abba yace ashirya da safe kowacce abita da akwatunanta, shi baiga dalilin ajiya ba. Duk sun amsa da to, amma kowacce burinta ace da ita aka kai nawa, Dan sunason suyo kallon kwaf, basu gamsu da labarin da 'yan kai amarya suka fad'aba akan gidana Dana munubiya, su a tunaninsu ma an aurenine domin a maisheni baiwa, yaushe nakai matsayin da har d'an Sarki guda mai sarautar Galadima zai gani yace yanaso, bayan lungu da sak'on hotunan mun gama zagaye duniya ni da shi. K'ilama da gaske yagama lalatani d'in. Haka dai sukaita gutsiri tsomarsu da kushe irinta masu hassada, duk da wasu abubuwan suna dawo kunnen innarmu batako damuba, ita dai babu abinda zatace ma ALLAH sai godiya, tunda 'ya'yanta kowanne yasamu matsugunni, yanzu saita maida hankalinta ga ibadar ALLAH da tarbiyar yaranta biyu maza dasuka rage, sune basu gajiba indai tozarcine. ★★★★★ Zuwa la'asar mama Fulani tafara k'ananun magana akan rashin nuna shaidar Munaya takawo budurcinta, dakuma rashin fitowarsu gaida mutane. ALLAH Sarki Aunty Mimi sai abin ya dameta ganin yanda aketa k'ananun magana a masarautar, hakkane yasata nufar sashen Galadima, babu zancen jiran a mata iso, sarkin k'ofa yabata hanyar tashiga. Tun'a falon farko daya raba sashina da nasa tace bayinta su jirata. Babu kowa a falonsa, Dan haka ta zauna tad'au waya ta kirasa, dan batasan halin dayake acikiba, baikuma kamata tashiga kai tsayeba, balle yanzu yanada mata. Fitowarsa kenan daga wanka saboda tashin dayayi a makare baisamu sallar la'asar ba, sai anan d'aki yayita sannan yashiga wanka. Wayar ya kalla yayinda yake goge ruwan fuskarsa, ganin aunty Mimi yasashi picking call d'in, saiya saka a Hans free yana cigaba da hidimarsa. “my aunty kin 6uya fa”. “na 6uya ko ka 6uya my k'ani, gani zaune ai a falonka”. “kai haba dai? to bani kamar 5minutes na shirya nafito”. “ok babu damuwa”. Bai wani dad'eba yafito sanye cikin farin boyal mai shara-shara, yayi k'au sosai, sai zabga k'amshin turarensa yakeyi na koyaushe. daga shi har Aunty Mimi suka sakarma juna murmushi, ya zauna kujerar dake kallonta yana fad'in “sweet aunty na ni kad'ai”. “anya kuwa yanzu bamu raba da Munaya ba my k'ani?”. Murmushi yayi wadda har hak'waransa na bayyana, ya d'ora k'afafunsa d'aya kan d'aya yana gyara zama, “in haka kikeso my Aunty saiku raba ai”. dariya tayi tace, “nama bar mata. wai kasan mike faruwa a gidannan kuwa?”. “A'a saikin fad'a”. “tun kafin tafiyar su mom aka fara k'ananun magana a masarautar nan, wai anzo kar6ar yankin mutuntaka ka hana”. “mtsoww!” yaja tsaki yana jingina da kujerar da lumshe idanunsa, “Aunty Mimi dan ALLAH karki biyema wannan jahilcin kema” yabud'e idonsa akanta, ransa a d'an 6ace yacigaba da fad'in “kawai da Wanda yakai sanin sirrinka da Wanda ma baikaiba wai duk sai sun sani?, a wace ayar alkur'ani ko hadisi akace dan ka tare da matarka a daren farko sai duniya ta sani?. ita mai aiko a d'auki k'yallen ince agaban kowa na gidannan lokacin da abunnan yafaru take fad'in bakinta bazai iya maimaita k'azantar danayiba?, to kuma tunda tariga da tasan nayi k'azantar abaya miye na aiko da wani k'yallen banza da wofi? wlhy fa suka kaini k'arshe zan shuka rashin mutunci kinji na rantse”. Shiru Aunty Mimi tayi tana kallonsa, tasan ransa yakai k'ololuwar 6aci, dan Galadima yanada hak'uri sosai, gudun kar matsala ta biyo saboda ciwonsa saita kwantar da murya, “haba my k'ani kwantar da hankalinka mana, ai abun bana 6acin rai baneba kaji, haba my habibi”. “Aunty Mimi nagaji ne wlhy, rashin mutuncin masarautar nan yafara isata, nifa komai zan iya kawoshi karshe a wannan karon”. Tasowa tayi ta zauna kujerar gefensa, ta kama hannunsa “please cool down mana my man, kaci gaba da hak'uri tamkar yanda kakeyi abaya, ALLAH yana tare da masu hak'uri, Momma bazataji dad'in wani Abu yabiyo bayaba, hakama Abie duk da yana a kwance zuciyarsa zatayi kunci, kansu ai sukema wa, yanzu ina k'yallen? ”. Iska ya furzar daga bakinsa, sannan ya nuna mata bedroom d'insa da hannu. Tashi tayi tashiga, a saman sofa taga k'yallen dan haka ta d'akko ta fito. zama takuma yi a kusa da shi, “my K'ani ina zamu samu syringe?”. Idonsa yabud'e ya kalleta, “syringe kuma? mizakiyi dashi?”. “Sameer duk abinda zamuyi mu kare mutuncin mahaifanmu da lafiyarka muyishi mu zauna lafiya. yanzu dai kasa wani ya kawo mana”. Baice komaiba yajawo wayarsa yakira Muftahu, buk'atarsa ya fad'a masa sannan ya yanke wayar batareda yajira cewar Muftahun ba. Wata hirar Aunty Mimi ta d'akko masa, tun yana basar da ita, har ya fara tanka ta, daga nan suka cigaba da hira. Knocking d'in k'ofar akayi, Galadima yace, “waye”. Sarkin k'ofa yace, “ranka ya dad'e yalla6ai Muftahu ne yazo yace amasa iso”. “kace ya shigo”. Da sallama Muftahu ya shigo, ya rissina ya gaida Aunty Mimi sannan yabama Galadima hannu suka gaisa cikin musabaha. Ledar hannunsa ya mik'ama Galadima, “no kabama aunty mimi”. Aunty Mimi ta kar6a ta fiddo da Syringe ta 6are daga ledar, had'awa tayi tare da Allurar sannan ta janyo charger ta d'aure tsintsiyar hannunta, Galadima da Muftahu dai kallonta sukeyi, allurar zata tsira Galadima ya rik'e “mizakiyi hakane Aunty Mimi?”. “Sameer! wannan itace kawai mafita, kabari kawai na d'iba a saka musu, da safe saika basu”. lips d'insa ya cije da k'arfi, yashiga kwance charger data d'aure hannunta, “ki barsa zan saka musu nawa, yanzu ma koda an saka zai bushene, dan yayi wuri ai”. “karfa kazo ka shukani”. “karki damu zanyi, kema kin sani ai, tunda na amsa to zanyin”. Mik'ewa tayi tana fad'in “shikenan to, bara na duba k'anwata itama”. Kansa kawai ya jinjina mata, yayinda muftahu yamata sallama ta fice. “wai mike faruwa? ranka ya dad'e”. Tsaki Galadima yaja, yay shiru kusan minti 2, har Muftahu ya yanke tsammani da samun amsa. labarin komai yabashi. Shima Muftahu tsuka yaja, “wai dan ALLAH yaushe za'a daina jahillar al'adarnan a masarautar nan? abinda ba addini ya wajabtaba sun kama sun rik'e, kuma duk matsalar tsohuwar nan ce wlhy, masarautu nawa ne suka daina wannan abun, amma mu takafa ta tsare, ALLAH lokacin da akayi na Uncle Hayatudden, kunya abinnan yabani saboda shi kawai nata6a gani, sashe-sashefa haka akaita nuniyar abinnan a masarautar nan wlhy”. Wani mugun tsuka Galadima yaja saboda haushi da abin yakuma bashi, fitarma da yay niya saiyaji yafasa. ★★★ Ni bansan mike faruwa ba ma, ina d'aki kwance duk kewa da kad'aici sun gallabeni, ga wayata babu caji saboda na manto cajan a gida. Nayi zurfi a tunani naji ana sallama. firgigit nayi sannan na amsa, hijjab d'ina najawo na saka, ina k'ok'arin tashi tashigo. da Sauri na mik'e ina mata sannu da zuwa, dan nariga da na shaidata itace aunty Mimi. rissinawa nayi na gaidata, ta amsa cikeda fara'a sannan ta zauna. mik'ewa nayi na nufi freight domin bata ruwan amma saita dakatar dani ta hanyar kamo hannuna. “no k'anwata barshi kinji, yi zaman ki, ya zaman kad'aici da bak'unta?”. Kaina a k'asa nayi murmushi kawai, sannan nace “Alhmdllh aunty”. “masha ALLAHU k'anwata, babu dai wata matsala ko?”. Kai na na d'aga mata alamar babu, daga nan mukayi shiru saboda rashin sabo. Zuwa can nace, “ina Samha?, tun d'azu tace zata dawo amma har yanzu?”. Murmushi tayi, tace, “sun fitane itada Sauban tun d'azun, amma nasan suna hanyar dawowa kam”. “Ayya ALLAH ya dawo dasu lafiya”. Ta amsa da amin tana mik'ewa. har falona namata rakiya, inajin dad'in yanda take nuna tana sona. ******* A can kuwa bayan Muftahu yafito daga wajen Galadima sai yayi murmushi, tabbas yasamu hanyar dazata zame masa tsanin *CIKAR BURINSA*, da wannan kawai zai iya cin galaba akan Galadima. Da wannan tunanin ya hau mota yabar masarautar gaba d'aya. Mikake k'ullawa ne Muftahu?😱 ★★★★★★ Bayan sallar isha'i ina zaune ina karatun Alkur'ani Galadima ya shigo, ban daina ba saida na kai aya sannan, na d'ago domin gaidashi sainaga idonsa a kai na. Janyewa nayi nace “barka da dare”. Bai amsaba cewa kawai yayi “tashi ki shirya zamuje gaisuwa cikin gida”. Nima sai ban amsa shiba namik'e kawai na maida Alkur'anin inda na gansa. tashi yayi yafita danya bani damar shiryawa. banja wani lokacin mai tsayiba nafito cikin Alk'yabba, tsaye na iskeshi a falona, batareda yace uffanba yafara k'ok'arin fita, nima sai nabi bayansa batareda na tanka d'inba.................✍🏼 🥳mun tafi sashen mama Fulani, maison jin yanda zata kaya saiya biyoni. ⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ Barka da juma'a😄🙌🏻 *_YA ALLAHA KA GAFARTAMA IYAYENMU_*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣4⃣ ............ Tunda muka fito masu hidimar sashensa suketa zubewa suna gaishemu, hannu kawai yake d'aga musu, nikam ma ba amsawa nakeba. Wata mota aka bud'e mana muka shiga, mamaki ya kamani, shin ba'a cikin gidan bane?. banida mai bani amsa dan haka nayi gum. Duk da darene muna ganin bayi dake yawo tsilli-tsilli, ga ko'ina kwanyar da haske, a k'ofar wani sashi ya tsaya da motar. Kallona ya juyo yayi, cikin muryar nan tasa ta k'asaita yace, “basai na fad'a mikiba, kinsan yanda ya kamata ace kowa ya ganmu, nan sashen kakarmu ne mai suna mama Fulani ”. Kai na na gyad'a masa, sannan muka fito saboda anbud'e mana dama tuni. Tunda muka fito ake kwasar gaisuwa, nikam sai binsu da kallon tausayi nakeyi, su shikenan a bautama wasu zasu k'are, basu da wani 'yancin Kansu...... Tunanina ya kakare, lokacin danaji tattausan hannunsa cikin nawa, kowannen mu saida yaji shock, nad'an rumtse idanuna, yayinda shikuma ya cije lips. Saida aka mana iso sannan muka shiga. kata faren falone na alfarma, iyakar k'yau da tsaruwa yayi, saikace ba falon tsohuwa ba, ga k'amshin turare na musamman na tashi,. Bafulatanar tsohuwace mai jikin fulanin asali, dankuwa akwai k'yawu iya k'yawu, tabbas wannan a zamanin k'uruciya anyi asalin k'yak'yk'awa, sai dai gajarta tamata tsiya kam🤣🤭. A kishin gid'e take, yayinda hadimai ke zagaye da ita, kowanne da aikin dayakeyi. Shigowar mu tasakasu kowa tasaki tanemi hanyar fita kamar yanda tabasu umarni. Bai saki hannuna ba har muka k'arisa gabanta, yayinda ita kuma idonta ke akan hannayenmu dake sark'e dana juna ko k'yaftawa batayi. Saida ya taimaka min na zauna bisa tattausan carpet d'in dake falon, gaf da mama Fulani kad'an, sannan shima ya zauna kusa dani. “Ranki ya dad'e barka da hutawa”. Nima sai bayi saurin gaisheta. Cikeda izza da tak'ama ta d'ago idanu tana kallonmu, a raina nace (ga wadda tafi Galadima izza ashe, ko dai itace sarkin😱?).. Kamarma bazata amsaba, saikuma naga ta gyara zamanta, idonta a kaina tana k'aremin kallo, “sai yanzu ka gadamar zuwa gaida mutanen saboda giyar amarci na kwasarka?”. Wani k'asaitaccen murmushi Galadima yasaki, Wanda ban ta6a Sanin ya iya shiba, “kusan haka ranki ya dad'e, kinsan masu iya magana kance amarya kota buzuzu🐝 ce d'okinta akeyi, bare ni kuma mai wannan dirarriyar macen doguwa k'yak'yk'yawa abun buk'atar kowanne namiji”. Idanu na zaro domin mamakin maganarsa, kakarsa yake fad'ama hakan?. maganarta Ce yaja hankalina itama........ Saida ta yamutsa fuska tana guntun murmushi, duk da maganar Galadima ta daki zuciyarta kwarai da gaske, ta kalleni da k'yau, “to ke dirarriyar mace abinda mijin naki yafad'a gaskiyane kuwa? dan mu bamu gani a k'asa ba”. Gabana yashiga fad'uwa, dan bansan mizan Ce mataba, 6oyayyiyar ajiyar zuciya na sauke saboda jin Galadima na bata amsa, dukda kuma amsar tashi itama tazomin a rud'ani. “to ranki ya dad'e miye amfanin gani a k'asan?, tunda nida ALLAH ya halattama ganin naga kayana”. Yanzu kam a kufule tace, “a titi ko?”. Ya murmusa yana kallona, “tunda Nina gani ai babu damuwa ranki ya dad'e, koda a titinne kuwa, bawai dole bane saike kin gani a gida ba”. Rasama mizata cemasa tayi, sai can tace inbanga na matarka ba ai naga na Uwarka da yayar uwarka ko?”. “well hakanefa ranki ya dad'e, amma nasan kafin kiga nasu, kema anga naki, so banga laifin hakanba ai”. Kutt, tsantsar 6acin rai na hanga a fuskar mama Fulani kuwa, nidai kam sun d'aure kai na da wannan zantuka nasu masu kama da gugar zana, wannan dai baza'a kirashi wasan jika da kaka ba, dan baimayi kama da wasanba, nataso gidanmu na yawa da tun ina k'aramata nagama sanin miye habaici miye gugar zana ko shagu6e. tabbas naji a raina akwai lauje cikin nad'i gameda wannan masarautar, dan tundaga zuwana zuwa yanzu naci karo da abubuwan mamaki bila adadin, ashe ba'a rabu da bukarba an haifi habu kenan, nabaro guguwar gidanmu na fad'a tarnak'in gidan sarauta mai wahalar zama, ni dai ALLAH ka taimakeni komai yafita filima kafin shekara d'ayarnan na kama gabana, bazan iya da kitimurmurar wannan gidan sarautar ba gaskiya. Mun mata sallama muka fito tana jifan Galadima da kalmar “fand'arrare mara mutunci, wlhy zanyi maganin kane, amma zan kira uwar taka naji idan itace ta baka wannan sak'on kabani”. Baice uffanba sai murmushi daya saki yakamani na tashi, munje bakin k'ofar zamu fita yajuyo yana kallonta, salute nata yayi sannan yace, “da safe za'a kawo miki jinin budurcin matata OK?”. Gaba nane yafad'i, da mamakin yanda yay furucin babu ko kunya bare shakka. nidai kam narasa yanda zan fassara wannan lamari, har muka shiga motar ina juya zantuttukansu a raina. Mun isa sashen dayafi kowanne sashe girma a gidan, sannan ya had'u iya had'uwa shima, Hadimai sunfi yawa anan fiye da ko ina, anan d'inma dai gaisuwar ce aketa mana. Mun isa wani k'ofar mai azabar k'yau, matar dake zaune a k'aramin falon farko ta rissinar da kanta tana fad'in “lale marhabin da Galadima, Gimbiya barkanki da zuwa fadar masarautar gagara badau”. Murmushi nayi na jinjina mata kai, amma gogan naku fuska a d'inke yace “Amana iso ga mai martaba idan bai kwantaba jakadiya”. “angama ranka ya dad'e, 6auna mai tafiyar k'asaita, bajimin zaki sa d'auka sa yak'i, magajin masarautar gagara badau........ Hannu ya d'aga mata alamar ya isheshi haka.. Ruf tarufe bakinta sannan tashige wata k'ofar, kusan mintuna 5 saigata yafito tana fad'in mu shigo. Jama'a karkuce nayi k'auyanci, tabbas ni Munaya yau naga daular duniya, dolene sarakuna suringa tunanin kamarma bazasu mutuba, yo irin wannan daular inbakayi yak'i da shaid'anba ai bautar ALLAH ma saika bari, dole suke halaka juna akan sarauta kam lallai. Wanda nakeda tabbacin shine sarki yana kishingid'e a kilisarsa, idonsa bisa TV yana kallon labarai, sai wata hamshak'iyar mace dake cikin ado na kece raini da alfarma zaune a gefensa, koba a fad'a makaba kasan matar sarkice. Yanzu ma har gabansu muka isa hannun na cikin nasa, dukda mutsu-mutsun kwata danakeyi yak'i saki, saima k'ara damk'ewa da yayi, nesa dasu k'ad'an muka zauna, cikeda girmama Galadima yace “barka da dare Abba?”. Murmushi sarki yayi, yace, “Galadima sai yanzu ake ganinka?”. Murmushi yayi yana shafa gefen wuya alamar jin kunya, ya kalli matar yace “barka da hutawa ranki ya dad'e”. Fuskarta d'auke da fara'a ta amsa masa.. Nima na rissina na gaidasu cikin tsantsar ladabi. Sun kar6amin fiye da yanda nayi zato, matar tamik'amin hannu alamar na matso gareta, banyi musuba na matsa, hannuna takama tana murmushi, “yaya bak'unta gimbiyarmu?”. Muryata a kunyace na amsa da “Alhmdllh ranki ya dad'e”. Murmushi sarki dake kallonmu yayi, ya maida kallonsa ga Galadima da shima idonsa na kanmu. “yarona babu dai wata matsala ko? ”. “Alhmdllh Abba babu komai”. “to Alhmdllh ai haka muke fata mu dama, ALLAH yayi muku albarka, yabamu zaman lafiya na har abada da zuri'a d'ayyiba, wadda musulunci da Muslims zasu alfahari da ita............” Nan yashiga mana nasiha mai ratsa jiki da 6argo, har lokacin hannuna na rik'e ga matar sarki, wadda k'amshin turarenta kemin dad'i sosai a hanci. Mun dad'e anan, dan sai kusan 9pm muka fito, tare da gagarumar k'yauta ta mukullin mota da sarki ya bani, matar kuma tace zata aikomin da tata insha ALLAH. daga ni har Galadima munyi godiya sannan muka fito, sai juya keys d'in nake ahannu inajin wani makahon dad'i, wai nice da mota har biyu, yanzu Abbana da Dady sun samu kenan, saura baba k'arami, dan nikam babu abinda zanyi dasu, iyayena zan baiwa. Daga nan munje 6angaren sauran Matan sarki, sai kuma na k'annen babansu Galadima d'in, mune har sashen da aunty Mimi ta sauka,, k'yaututtuka dai nasamesu sosai, harda masu sark'ok'i da sauransu, mun dad'e annan fiyema da ko ina, dan har 12 muna can, sunata hira tsakaninsu, danni dai ban iya cewa komai, sai sun sakoni ne nakanyi murmushi, musamman Sauban sarkin tsokana da Samha sarkin surutu, galadima kam ba komai yake tankasuba, shida aunty Mimi ke maganarsu jefi-jefi, khaleel ma sanda mukaje yayi barci. saida aunty Mimi tace mutashi muje sannan muka dawo namu 6angaren. Sai da yarakani har d'akina sannan ya juya yafita batareda yace uffanba. Binsa kawai nayi da kallo ina sauke ajiyar zuciya. Ni ban ta6a ganin murd'ad'd'en mutum irin wannan mutuminan ba, wlhy miskili yafishi dad'in zama, danshi na lura ba muskili baneba, tsabar jin kai ne kwai ke d'awainiya dashi. ★★★ Shikam har yayi shirin barci yagama yay shafa'i da wutiri maganar Mama Fulani na caccakar masa rai, ya murmusa kawai saboda takaici, ya zauna saman kujera d'akin, Syringe d'in d'azu ya d'akko da k'yallen yana jujjuyawa a hannu, wani sashe na zuciyarsa na cewa kawai yayi dabaran Aunty Mimi, wata kuma nacewa kar yayi tunda ba addini baneba, koma Dan ya k'ular da zuciyar mama Fulani, to amma kuma ita yarinyar za ana kallonta wani iri ai kuma a masarautar, harma sudunga tunanin ta zubar da mutuncinta a wajene kamar yanda mama Fulani tace, gara yayi kawai dabarar Dan fatansa harsu rabu baya son wani abu na family d'insa ya shafeta. Wannan shawarar da zuciyarsa ta yanke masa yasashi jawo charger ya d'aure hannunsa, jijiya ta bayyana, ya rintse idonsa yayinda ya tsira allurar, cikin cije lips yaja jinin kad'an sannan ya zare ya danne da auduga yanajan tsaki, charger d'in ya kwance yay wurgi da ita saikace itace tamasa laifin🤣🤭. d'aukar gyallen yayi ya yamutsashi da hannu duk yayi Squeezing sosai sannan ya matse jinin ajikinsa yad'an yayyarfa bayan yazuba shi awaje d'aya da yawa. sai wani yamutse fuska yakeyi tamkar yaga kashi, kokuma jinin ba daga jikinsa yafito ba. ya ajiyeshi gefe sannan yamik'e yafito, a duzben d'in falo ya saka syringe d'in da kad'ar yakoma ciki, saida ya wanke hannunsa sannan ya haye gadonsa ya kwanta yana wani 6ata rai. Nima can bayan na kammala hidimata kwanciyar nayi cikeda kewar 'Yar uwata, yauma nadad'e banyi barciba, sai daga baya ya saceni. Washe gari bansan miya faruba naji busar algaita na tashi a k'ofar sashenmu, yayinda aketa cillara gud'e-gud'e dake tashi, ina niyar fitowa domin ganin abinda ke faruwa Galadima yashigo da d'an hanzarinsa, hannunsa d'auke da k'aramin tire da kofin shayi akai. “hau gado ki kwanta” yay maganar yana ajiye kofin a table d'in gaban gadon. “miya farune?”. na tambaya cikin binsa da kallo. “ok zauna tambayata har su shigo ciki, oya malama ki hau”. Nidai duk mamaki ya isheni, kamar wadda aka make haka na hau gadon na zauna, kallon face d'ina yayi yaga babu wata alamar dawani zaiga nashiga wani hali, dolene ya canja yanayina kenan idan har yanason ya tsira daga kwakwaf d'in wannan shirmen kafin su shigo. Kawai sainaga ya hayo gadon shima, kuma kaina yayo gadan-gadan, na bud'e baki da nufin tambayarsa dalili, kawai naji bakinsa cikin nawa. tsorone ya kamani da fargaba, sai kawai nahau dukan bayansa da k'ok'arin turesa, haka dama yakeso, yazam nayi yunk'urin kwatar kaina har nad'an jigata yanda kowa zai d'auka wahalar daren jiyanne. kuma rikicewa nayi saboda wasa daya fara da wasu 6angare na jikina,, so kawai nake na kwaci kaina awajensa, tun ina iya yunk'urin turesa harna kasa, dama nima nasan ganganne na iya da wannan basamuden mutumin🤣🤭 (munaya tafad'a ba niba😂⛹🏻‍♀). Sai da yaga nayi lakwas ina hawayene kawai na daina tureshi sannan ya d'agani yana sauke numfashi, nikam saina kuma fashewa da sabon kuka, (kai jama'a Galadima akwai bariki😱🤭) yanajin takun isowar su Fulani da kirarin kuyanginta sai yayi saurin jan bargo ya rufamin zuwa cikina, yawani kwantar da murya yana fad'in “please my jannat kiyi hak'uri hakanan, kukan ya isa kinji, tun daren jiya kike Abu d'aya, haka ai kowacce mace tayi sannan tazama uwa, ALLAH dai yayi miki albarka, kifad'amin wace kauta kikeso saboda tukuycin budurcinki daki kawomin har gidana”. Idanu nad'an zaro saboda tsorata, mi wannan gayen yake nufi? wai ko dai Galadima yana shaye-shayene ban saniba, abunda yazo yamin daban sannan yakuma d'akkomin wani zancen daban......... Gyaran muryar da akayice yasamu waigawa ni da shi, kakarsa ce ta jiya a atsaye dawasu mutane biyu, gabana ya fad'i da matsananciyar kunyar su, Dan inada tabbacin sunji ko sunga abinda yamin, ko dai saboda su yake wannan abun? da sauri naja bargon na rufe fuskata saboda kunya. Yayinda shikuma ya kalli mama Fulani yana wani susar gefen wuya kamar gaske, “o ranki ya dad'e kune? bar kanku da zuwa Ku shigo mana, saima Ku tayani lallashi ai”. Matannan buyu gud'a suka callara a tare, yayinda mama Fulani ta kafama Galadima idanu, alamun tuhuma. kansa ya d'ago shima suka kalli juna ya sakar mata wani lallausan murmushi, kafin ya janye idonsa ya maida a kaina danake k'udundune cikin bargo. d'aya cikin matan ta rissinar da kanta, cikin girmamawa tace, “Ranka ya dad'e ko zaka bamu waje mu k'imtsa ta?”. Kallonta yayi, fuskarsa d'auke da murmushin Dana sakama suna na rainin hankali, cike da k'asaitarsa yace, “na hutasheku jakadiya, danni tun a daren jiya na gyara matata”. Mama Fulani dake kallonsa a zuciyarta tace amma dai yaronnan d'an rainin wayone wlhy, gaba d'aya ya shirya komansa dai-dai ta yanda babu wanda koda ta k'aryata zai yarda da ita, Dan tabbas tasan duk k'arya yakeyi gameda wannan k'yallen, gashi lungu da sak'o na gidan angama nuna k'yallen, saboda ma ya raina mata wayo ba 6angarenta aka kaiba, sashen matan sarki ya aika da k'yallen, zancennan ma da akeyi ita bataga k'yallen ba har yanzun, Dan ba'a kai mataba, kowa ya d'auka daga sashenta ya fito, tunda ita ake fara kaimawa tagani sannan Matan sarki. Had'a ido sukayi da Galadima, bakin ya ta6e mata, tareda d'age gira sannan yasaki murmushin Dake k'ular da mama Fulani aduk lokacin da yayisa. Ta had'iye wani yawun bak'in ciki tareda kauda kanta gefe, su jakadiya kam tuni sun yi nisa wajen kar6o k'yaututtukan da kuyangin kowane sashe ke kawowa daga Matan gidan da iyaye, duk abama Munaya. Dole mama Fulani ta k'arasa gaban gadon tasakama munaya turare da Sanya mata albarka tamkar yanda al'adar gidan ta tanadar, sannan takama hannunta ta saka mata bangles na goal masu k'yau da d'aukar idanu. Ta shafa kan munaya tana murmushin yak'e. sannan tadawo gaban Galadima shima takama hannunsa ta d'aura masa agogon Azurfa mai k'yau. Salute nata yayi yana fad'in thanks my sweet Granny ”. Uffan batace masaba tajuya tafice daga d'akin. yayinda su jakadiya suka take mata baya. Suna fita ya sauke ajiyar zuciya tareda dafe kansa yana jan tsaki, nima kaina na bud'e amma nakasa tashi saboda kunyarsa data dabaibayeni. Kusan mintuna 5 muna a haka, ni inata hawaye da jamasa ALLAH ya isa a zuciya, ga la66ana sai zugi sukemin saboda Sumbata d'inma na mugunta yamin. shikam yana dafe da kansa har yanzun yana sauraren kukan danake rairawa. Zamansa ya gyara ya juyo yana kallona, fuskarsa a matuk'ar d'aure yace “tashi ki zauna muyi magana”. Yanda yay maganar yasani tashi zaune batare da na musaba. Yad'an kalleni ya janye idonsa sannan ya mik'amin Handkerchief d'insa daketa tashin k'amshi alamar na goge hawayena. Kamar bazan kar6aba dai saikuma na kar6a na goge fuskata. Nanma shiru mukai nawasu mintuna da basufi 2 ba, nakula magana yakeson min amma yanata mulmulata a zuciya saboda jin kai, kuma d'agowa yayi ya kalleni saikuma yay gyaran murya kad'an, “em kiyi hak'uri, bamuda wata mafita sai wannan, munada wata kidahumar al'adane a masarautarnan, dolene randa katare da matarka sai kowa yasani ta hanyar ganin jini ajikin k'yallen da aka shinfid'a muku a gado. mukuma namu auren yasha banban dana saura, banida niyyar zalintarki na maidaki bazawara sannan na sakeki, inason idan mun rabu duk mijin daya aureki yasameki cikin mutuncinki, shiyyasa bazan aikata abinda suke buk'atar ba. ajiya anta surutu saboda bamu bada wannan shaidar ba, shiyyasa a Daren jiya nayi wata dabarar daban, fitowata kenan daga wanka najiyo busar algaita da gud'a alamun k'yallen yagama zaga masarautar, shiyyasa nayi azamar d'akko coffee d'in da aka had'amin zansha nanufo nan dashi, Dan Muftahu yakirani ya sanarmin zafa azo har sashena domin sanyamiki albarka da k'yaututtuka dakika samu saboda kin kawo mutuncinki, yanayin dana ganki nasan zasu gane shirina, shine dalilin yimiki wannan abun dan fidda zuciyarsu daga zargi, karki d'auka nayi mikine da niyya koki kalleni cikin mutane masu sa6a alk'awari”. yana gama fad'a yamik'e zai yafice, nidai kaina ak'asa jinake tamkar namasa masifa amma kwarjininsa ya hanani, saida yaje bakin k'ofar zai fita sannan ya kuma furta “kiyi hak'uri, Sameer baya zalunci”. ya ida ficewarsa kawai. Duk da na yarda da abinda ya fad'a, hakan bai hanani rushewa da sabon kuka ba, nace mugu kawai ALLAH ya isana wlhy, na shafa la66ana da da haryanzu zugi sukemin suda k'irjina wlhy, dan tsabar mugunta shine yama tsaya iya bakin amma harda wani wajen, ALLAH ya isana nidai. 🤣🤣kujifa, mutum da sadakinsa Munaya ke kiransa da mugu da jamasa ALLAH ya isa😂, yau munga auren Contract readers😝⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Tunda abunnan yafaru bamu sake had'uwa da shiba a ranar da yinin washe gari , kullum dai Samha kan kawomin abinci tareda kuyangin Aunty Mimi. ★★★★ Bayan sallar isha'i damuwa da rashin jin innarmu da Munubiya ya gallabi zuciyata, jinai bazan iya daurewa ba, dan haka na yanke shawarar zuwa na rok'esa ya aramin charger kona samu nayi charge wayata, duk da ma banida isashen credit aciki. na d'au turare nad'an fesa kad'an sannan nazura dogon hijjabi nafita zuciyata na d'ar-d'ar. Na dad'e k'ofar falon tsaye ina tunanin yanda zan shiga, daurewa nayi nai Knocking, wata murya naji ta amsa sa6anin tasa, akace “waye?”. Saida gabana yad'an fad'i, cikin rumtse idanu nace “nice”. Galadima dake kwance cikin kujera idonsa a lumshe yana sauraren Muftahu yabud'e idonsa da sauri. Shikam muftahu cewa yayi “bismillah ranki ya dad'e, ki shigo”. Na tura k'ofar ahankali na shigo da wata sabuwar sallamar, Muftahu ne kawai ya amsa cikin washe baki, (yayinda k'asan zuciyarsa ke wata iriyar murna ganin shirinsa zai tafi dai-dai kenan). Galadima kam idanu kawai ya zubamin cikeda mamakin miya kawoni?. Gaisawa mukayi da Muftahu cikin mutunci. saiya mik'e yana fad'in “ranka ya dad'e nikam na wuce, zuwa Safiya zamu k'arasa maganar kawai”. Kansa kawai ya d'agama Muftahu n. Muftahu ya kalleni yace “gimbiya mu kwana lafiya”. Na murmusa sannan na amsa da “to ALLAH ya tashemu lafiya”. Koda Muftahu yafita sainayi tsaye nakasa magana ganin ya zubamin idanu, ganin banida niyyar magana saiya nunamin kujera alamar na zauna. shima yana tashi zaune sosai. Ban musaba na zauna. “miya faru?”. ‘yafad'a yana zuba Hollandia fresh milk a glass cup d'in gabansa”. d'agowa nayi nad'an kallesa, dai-dai yasaka kofin a bakinsa zai sha, janye idanuna nayi ina kuma had'e fuska. aransa yace kai wannan yarinya akwai jan ajin tsiya. Saida naja wasu seconds sannan nace charger zaka aramin please, nabaro tawa a gida, gashi inason waya da munubiya da innarmu. Crossing kafarsa yayi yana cigaba da shan free milk nashi tamkar bai jini ba, harna fidda tsammanin zai tanka min, sainaji yace, “ina wayar?”. yay maganar da mik'omin hannu alamar na bashi Mik'ewa nayi na kai masa wayar ina tunanin mizaiyi da ita?. Koda ya kar6a saiya mik'omin cup d'in hannunsa bayan yak'ara fresh milk d'in a ciki. Na girgiza masa kai alamar na k'oshi. wani kallo ya watsamin daya sani kar6ar dole. nadawo mazaunina na zauna, inata rik'on cup d'in amma nakasa sha, haka kawai naji hankalina bai kwanta da fresh milk d'in ba, bawai zargin yazuba wani Abu nakeba, haka kawai dai banjin sha. Shikuma ya basar dani yanata juya wayar kawai a hannusa, basan miyake kalloba ajikinta. Kallona yayi yace, “kin rik'e Number su?”. “eh” nafad'a batareda na kallesa ba. Wayarsa ya d'auka guda d'aya ya had'omin da tawan ya mik'omin, “kije kuyi wayar kawai, da safe sai a nemo miki charger d'in”. Na tashi naje na kar6o tareda cewa “nagode” najuya nafice da cup d'in fresh milk d'in a hannu na. Bina yayi da kallo harna fice, ya sauke ajiyar zuciyata kafin ya cije lips nashi domin jin mararsa tad'an rik'e masa kad'an. Koda naje d'akina saina kasa ajiye fresh milk d'in, haka kawai naji kuma sha'awar nasha, nako d'aga cup d'in na shanye tas sannan na zauna ina juya wayar tasa datamin k'yau, saina tuno wayarsa daya barmin ranar idi, na ta6e bakina kawai nafara saka number innarmu..............✍🏼 Hummm mi zai biyo baya bayan shan fresh milk kuma?. da zuwan muftahu?.🤥 Wannan amsar sai ranar Monday🤫. naso yimuku wannan weekend d'in amma munada biki gsky.😄💃🏻 *_hhhh naji k'orafinku sister's, ammafa ko pages biyu nakeyi ba isarku zaiyiba😄, wlhy bama nida time d'in yin typing 2pages a rana, saboda inada aure, akwai nauye-nauye a kaina nima, masu kuma so nagama kafin azumi suma ina basu hak'uri, bazai yuwu nagama kafin azuminba, dan azumin kad'an ya rage, kuma banason datse labarin nan kamar yanda nayi a SIYASA KO KABILANCI, zanbi a hankali na gama, wlhy nafiku son nagama nima Na huta, Dan dana fara buk zai fara cizona a zuciya nima, so kawai nake naga nagama😄, karku manta ko tarihin masarautar su Galadima sameer har yanzu bamu saniba, Dan haka zamuyi, iya inda muka tsaya saimu cigaba bayan salla idan ALLAH ya kaimu da rai da lafiya, Dan kamar yaune ai.😄👌🏻._* Ngd sosai da soyayyar dakuke nunama buk d'innan, ina sonku nima har cikin raina, ina fata zaku fahimceni😄👌🏻. ❤❤❤❤❤❤❤ ⛹🏻‍♀ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭👏🏻_* *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣5⃣ ..........Bugu biyu ta d'auka, jinayi tamkar anmin bishara da aljanna dan dad'i, lokacin danaji muryar innarmu tayi sallama cikin sanyinta sai kawai na Sanya mata kuka. Ita kuma daga can batasan wayeba, a sanyaye tace “baiwar ALLAH ko bawan ALLAH lafiya kuwa?”. Murmushi nayi, gakuma hawaye na kwaranya, nace “innarmu nice fa”. Cikeda d'okantuwa tace, “Munaya kece? ya kuke?”. Murmushi nayi mai sauti, nace “innarmu ina yini? inasu Aryaan? Wlhy ina missing d'inku innarmu, ALLAH kamar na dawo gida”. na k'are maganar da sakin kuka. Kallon juna sukayi da Abbanmu, da yake girkin tane tana d'akinsa, sukama juna murmushi, Abba yace, “haba dai munaya ta jaruma ce da kuka haka? Ina aka ta6a kai mutum gidan miji yayi sha'awar dawowa gida inbada yawoba?”. “wayyo Abbanmu I miss u so much kaima wlhy”. Dariya suka sanyamin shida innarmu, Abba yace, “yo ga sakaran yarinya, miyeto na kukan hakan? Yaya mijin naki da jama'ar gidan?”. “komai lafiya lau Abba, sai kewarku, musamman ma Munubiya, ALLAH ina kewarta Abba, dan ALLAH kace ya kaini na ganta”. Yanzu kam dai su Abba sosai sukemin dariya, saikuma suka shiga tsokanata, tun ina kukan harna ware nima ina dariya, munyi hira sosai, kafin Abba yace “saida safe hakanan, karda ki k'are masa kud'in, ki gaidashi”. Cikeda farinciki namusu sallama, da cewa zankirama gobe. Na yanke wayar ina murmushi, Munubiya na kira itama, cikin sa'a tashiga kuwa. tana kwance jikin yaa Marwan yana d'an rage zafisa🤫, wayar tafara ring, shine yamik'o mata, ta amsa tana kallon number, irin Special number d'in Nance, wadda zaka ganta a tsare. (🤫bara na Baku, amma banda matan aure 07000000000😝)⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Saida ta kalli yaa marwan ya d'aga mata kai alamar tayi picking sannan ta d'aga. Muryar Munaya dataji yasata mik'ewa zaune zumbur cikeda d'oki. Kowa yay kewar d'an uwansa, dan haka ko gaisuwa bamu tsaya yiba muka shiga fad'ama juna yanda mukai missing. muka 6alle hira kamar zamu ga juna tacikin wayar.. Mun d'au tsawon lokaci munayi kafin yaa Marwan yasamu dole yin sallama, wayar ya kar6a ya jawo matarsa ya rungume, zatayi magana ya d'ora yatsansa a bakinta alamar tayi shiru tareda yanke wayar ko sallamar arzik'i bamuyiba. Inajin sukur-sukur d'insu ta wayar, dan haka na tuntsure da dariya ina fad'in oni su yaa marwan Ashe dai ashe?....😂🤭. Number Fauziyya na gwada itama akashe, nace lallai amarci yayi dad'i kenan?, itama Ayusher na kira number busy, 'Yar tara, nasan tanacan itada khamees ana soyewa. Feena ma wayarta Switch up, nad'anyi tsok'i na ajiye wayar Na tashi domin yin shirin barci, dan yau ina cikin farin ciki, tunda naji muryar families d'ina. Tun bayan fitar Munaya kam Galadima yafara jin canji a jikinsa, a hankali yakejin wani feelings na bijiro masa, kamar wasa abufa yafara tsamari, tun yana basarwa har mamaki yafara kamashi, shin wai mike faruwa ne dashi haka? bazaice baya sha'awa ba, yanayi sosai, dan wani time d'inma saiyasha tablets, ko allurar kwantar da sha'awan, amma baita6a jin irin na yauba, k'arfin sha'awarsa yasashi katange kansa daga dukkan abinda zai iya zurmasa ga halaka har yazama hanyar tsanin aikata zina. duk da jiya yad'ansha wahala saboda abinda yafaru tsakaninsa da yarinyar can duk da shi yayine badan yaji wani abuba, amma Abu yaso zamar masa Matsala a yinin gaba d'aya, sai dai tunda yaje yay allura sai nutsuwa tazo masa. Dauriyarsa ce take Neman zuwa k'arshe, sai kawai jikinsa yafara rawa, da bin bango yashiga bedroom d'insa, drowan gefen gadomsa yabud'e yad'iba drugs kusan uku ya watsa a baki, ruwa ya d'auka frigate ya korasu suka wuce. Humm abanza wai man kare, maimakon yaji sauk'i saima abin ya k'aru. yadawo falo saman doguwar kujera Yakuma kwanciya bayan ya kashe AC n gaba d'aya, Dan k'ara dulmiyar dashi yakeyi. Nima d'in agareni kusan hakane, kad'an-kad'an nafara jin tsigar jikina Na tashi. Kamar wasa ina wanka sai Abu yafara shan kaina, abinda bansan ma'anarsa ba yafara bin jinin jikina da 6argo, na lumshe idona ina hango abunda yafaru tsakani na d'azun da Galadima, duk dani wahala ma nasha, wani feelings na tashin hankali yafara bijiromin, idanuna harsun sauya kamanni, da k'yar nayi wanka nafito, ko towel d'in ban cireba na saka hijjab Na d'au wayarsa Na fita, koda nayi sallama a k'ofar falonsa banji ya amsa ba, nayi har sau uku shiru kakeji, shikam yana kwance yana jina, amma bakinsa yakasa koda motsawa barema ya amsa min, saima muryata dake sakashin jin wani zirrr, duk sanda nayi sallamar sautin muryata na motsawa da tsigar jikinsa ne, gaba d'aya gashin jikinsa ya tashi. Jin shirun yayi yawa natura k'ofar kawai Na Shiga abuna, azatona ko barci ya d'aukesa kokuma bai jiniba. Ganinsa kwance saman doguwar kujera yasa gabana d'an fad'i, gawani iri dana kuma ji jikina yayi, dagashi sai boxer da vest, hannunsa d'aya dafe da mararsa, d'ayan kuma dafe da kansa, kauda kaina nayi daga kallonsa saboda tsorata da ganinsa a ainahinsa, gaskiya ba k'aramin namiji bane guy d'innan, duk kunya ta isheni, ban ta6a ganin namiji ba a haka, yo samarin gidanmu basa zama haka. duk tunanina barci yakeyi, na ajiye wayar saman cikinsa a hankali, kamar yanda naga d'ayar a ajiye, caraf ya rik'e hannuna da hannunsa daya dafe kansa, tsoro yakamani lokacin daya bud'e idonsa yana kallona, jazur idon yake abin tsoro. Muryarsa a matuk'ar sanyin daban ta6a Sanin yana da shiba yace “mi zakiyi?”. idanu na nad'an waro waje cikin tsarguwa nace, “mi zanyi kuma? wayarkace fa na ajiye maka”. ajiyar zuciya yad'an sauke, ya zuba min idanu batareda yasakimin hannunba. Gaba d'aya jikina yakuma rikicemin, jima nake tamkar Na fad'a kansa saboda abinda nakeji, ganin karna aikata abinda zanzo ina nadama saina zare hannuna dad'an k'arfi, jikinshi babu kuzarin kirki, danhaka yasaki hannun kawai, nikuma na juya nafice daga d'akin da saurina. Lips d'insa ya cije da matuk'ar k'arfi kamar zai huda, Yakuma dafe mararsa datayi tamkar zata fashe masa, kai bazai iya daurewaba, domin zai iya mutuwa wlhy, ganin yarinyarnan kuma Yakuma birkita tunaninsa. idonsa yarigada yarufe, ya manta matsayin Auren Nasu, duk da gargad'in da wani sashen zuciyarsa yake masa akan alk'awarin daya d'auka, burinsa kawai ya sauke wannan nauyin kozai samu nutsuwa, da k'yar yamik'e ya fice zuwa d'akina. Nikam INA zuwa na zube saman gado bayan Na zare hijjab d'in, dagani sai towel, marata data d'aure tamkar zata fashe na rik'e da hannu biyu Ina hawaye, wai wannan wace iriyar masiface ne?, nashiga uku ni Munaya, mike shirin faruwa dani ne?.. “innalillahi” kawai nake iya karantawa saboda tashin hankali, jikina harwani rawa yakeyi, ko kad'an bansan Galadima ya shigo d'akinba, dan nafad'a wata duniya ta daban, babu zato kawai naji mutum yafad'o jikina yana sauke numfashi wani na k'orar wani, wata wawiyar runguma yamin tareda matseni ajikinsa gam, kai kace cikinsa zai maidani. Humm maimakon na turesa sai nima nakuma k'ank'amesa, banyi k'asa a guywaba wajen maida masa murtani abinda yakemin.. Daga ni harshi kowa yafita hankalinsa, dan idonmu yarufe bamusan mi Muke aikatawa bama. Hankalina bai nemi dawowa ba saida naji Galadima na neman kasheni, duk da inajin lokacin dayake jero addu'a amma ban dawo dai-daiba, nayi nisan da banajin kira kam, saida mai gayya mai aiki ke shirin faruwane na farga. Ina yayi Nisan da bazaiji kiranaba balle kuka da magiyata akan karya cutar dani, yatuna alk'awarin daya d'auka please, baimasan inayiba, duka, cizo, yakushi, babu kalar da ban masa ba, amma bawan ALLAH nan saida yamin biji-biji, dukkan fushinsa na shekarun baya saida ya fanshe a wannan daren. Nayi kuka harma ba'a jin sautin fitarsa, a jama'ar gidanmu kuwa ai mutum d'ai-d'aine ban kiraba, duk tsanar innaro danayi ranar saida nakirata ta taimakeni (🤣Munaya anga idi😝). ★★★*★*★*★★★ A can kuwa muftahu Na fita sukaci karo da Harun, kallon-kallo akama juna, cikeda tsantsar mamaki Harun yace, “wai Muftahu mikake shiryawa ne?”. Kallon rainin hankali muftahun yamasa, yagyara tsayuwarsa yana wani murmushin da bakowa zai iya fassara Shiba, “ban fahimci tambayar takaba, amma mikake nufi?”. Harun ya d'an hararesa, “Muftahu karka rainamin wayo, tabbas nasan ni da kai duk abokan Galadima ne, bayan zumunta dake a tsakaninmu, amma shige masan dakake fiye da kowa a wannan tsakanin yana bani mamaki”. Muftahu ya ta6e baki yana wani basarwa, kafin ya kalli Harun a wani yanayi, “Harun kana sakamin idone kenan a al'amurana? humm bazance ka bariba to, kacigaba, ni da kai d'an halak ka fasa, idan kaga dama ka kunna wutar jefani bayan kaga abinda zanyin, wannan ba damuwata baceba, inar Na cimma burina right?”. yana gama fad'ar haka yabar wajen kawai. Yayinda Harun yabishi da kallo kawai tamkar wani soko, a zuciyarsa yana tunanin mi Muftahu ke shiryawa ne akan Galadima? tun kwanaki yakeson fargar da Galadima illar kusanta Muftahu a jikinsa, amma abin kamar wani tsafi, da Zarar sun ke6ance da Galadima to saikaga Muftahu a wajen, saikace mai gani har hanji, kenan yakamata yasake shiri akan Muftahu?. Da wannan tunanin shima yashige mota yabar gidan, saikuma Galadima ya fad'o ransa, waya ya d'auka ya kirashi, amma saiyaji Number busy, hakanne yad'an sakashi nutsuwa, a tunaninsa ko Galadima yana wayane dasu Momma. (A time d'in Munaya Na waya da phone d'in Galadima). ★★★*“*“★”*”*★★★ Yanda ta tashi a firgice haka shima ya tashi, jikinsa ya jawota ya rungume saboda waige-waige da takeyi tana kwala kiran sunan MUNAYA!. jinta a jikinsa saita d'an sami nutsuwa, cikin kuka tace, “yaa marwan mike faruwa da 'yar uwata ne?, nayi mafarkinta cikin mawuyacin hali tana kuka da kiran sunana Nazo Na ceceta”. “sorry baby, ki kwantar da hankalinki mafarki ai ba gaskiya baneba, maybe shaid'anune kawai suka taswuranta hakan a gareki, amma ba d'anzun kuka gama wayaba? kofa awa 5 ma ba'ayiba da gama wayar taku?”. “hakane yaa marwan, amma acikin awa 3 wani Abu bazai iya faruwa ba? ka kiramin ita please naji?”. “no kiyi hak'uri, dare yayi gaskiya, babu yanda za'ayi mu kirata a wannan time d'in, k'arfe 1 fa ta wuce, 2 ma saura, karkuma ki manta tanada miji itama yanzu. Muyi addu'a ALLAH yasa alkairine, da safe saiki kirata ko?”. Cikin share kwalla ta d'aga masa kanta, a hankali ya kwantar da ita a jikinsa bayan shima ya kwanta, yad'an furzo huci kafin yakai hannu yana shafa kanta tareda sumbatar goshinta yacigaba da bubbuga bayanta a hankali, kowa yana yin adu'a, ahaka barci ya kwashesu, duk da sun dad'e basu koma ba, musamman ma Munubiya da mafarkin yak'i barin ranta, Dan takasa yadda Munaya Na cikin k'oshin lafiya gaskiya, ka wai dai dan batada yanda zatayine ta hak'ura. *****★★★*★★★**** Hawaye kawai nake iya zirarwa, amma kwakwkwaran numfashi bana iyawa saboda jigata, zan iya danganta abinda Galadima yayimin da fyad'e, dan baya cikin hayyacinsa ko kad'an, kamar yanda nima nawa ya gushe daga farko nabashi gudunmawa. (Nasan duk mai hankali ya k'iyasta a yanda Galadima ya zomin zai tabbatar dolene na jigata d'in😭). Tunda yasamu nutsuwa yana gefena a kwance kawai, a hankali memory d'in brain nasa ke tariyo masa abinda ya aikata tamkar a mafarki, ya bud'e idonsa da hanzari akaina, domin kuma gaskata abinda yafarun, shin da gaskene ya aikata? “innalilahi” yashiga maimaitawa dan ganina kwance a gefensa ina hawaye, daganin yanda nake a kwancen ina fidda numfashi d'ai-d'ai kasan nagama jigata, yabi d'akin da kallo cikin tsantsar takaici, yaushema shikam yazo d'akinnan? “Hasbinallahu wa ni'imal wakil. mike faruwa danine ni Sameer? wace k'addarace kuma ta kutsoma rayuwata? yanzu nan ni Muhammad Sameer ne da wannan d'anyan aikin? miya samu tunanina haka?.......” Tunaninsa ya tsaya cak lokacin daya jiyo dasashshiyar muryata ina kiran innarmu da Munubiya, muryata a raunane, runtse idanunsa yayi tareda mik'ewa zaune da k'yar, dan jikinsa gaba d'aya yayi week, ga wani masifaffen ciwo da kansa keyi. da k'yar ya iya kuma bud'e idanunsa a kaina, babu shiri yakuma runtsewa saboda tsorata da ganin yanda yamin, hawaye kawai yaji suna neman zubowa a face nashi saboda shi mutum ne mai tausayi, bayason yaga ancutar dawani bare kuma shi da Kansa ya aikata, jarumtar had'iyesu yayi tareda kuma bud'ewa, yazubama fuskata ido batareda ya iya cemin uffanba, yama rasa ta inane zai fara shikam, mizai fad'amin kuma a yanzu Na yarda dashi? mizai cemin shikuwa?. Innarmu dana sake ambata murya a sark'e yasakashi saurin kallona, baisan yarik'o hannuna ba ya rumtse anasa, la66ansa sai motsawa suke amma yagaza yin magana, shi yanzu ma baisan wane irin taimako zai baniba, bai ta6a irin hirarnan dawani abokiba balle yace yasan ya zaiyi, bai ta6a aikata zinaba, zai iya rantsuwa da Ubangijin daya haliccesa bai ta6a ta6a jikin wadda ba muharramarsa ba, sai ita Munayar daya d'auketa randa yasa a sato masa ita. Kuma ko muharramar tasa bazai wuce yarik'e hannun taba shima ba kowaba wlhy, inhar kacire Samha Momma Aunty Mimi ko Mom, sukad'aine mata Muharramsa da zaice yanada shak'uwa ta musamman dasu, amma shi ko yaran masarautar nan bama kowacce zai iya ambatarta da sunanta dai-daiba..... Rashin ya cika da tashin hankali, kukan danakeyine yasakashi waigen phone nashi, baiga komaiba, tunawa yayi ba d'akinsa baneba nan, ya saki hannuna ya sakko agadon bayan ya suturta jikinsa, jikinsa gaba d'aya ya mutu, ahaka da sand'a yakai falonsa, wayarsa dake a saman kujera ya d'auka, to inama zai dosa shikam? wazai kira akan wannan abin kunyar daya aikata? tunanin bincike a network ne ya fad'o masa a rai, maybe yasamu bakin zaren, Google yashiga yay d'an rubutu yahau Searching, amamakinsa kam saigashi sun bashi, saiya kuma wata tambayar, nanma yasamu amsa dai-dai, “Alhmdllh” yafad'a yana mik'ewa rik'e da wayar. Inda yabarni ya iskeni, Toilet yawuce kai tsaye, yayinda nabishi da kallon tsana, nikad'ai nasan minakeji akansa, ayanda nakeji ko wuk'a aka bani zan iya fidda masa hanji waje, tabbas yanzu nakuma yarda banida wayo, yanda tun farko Na yarda da maganar wai auren yarjejeniya mukayi da Wanda yafi k'arfin ajina da matsayina, inma banda wauta irin tawa tayaya mutum kamar Galadima zai nemi kulla aure dani?, Na manta namiji zai iya komai domin cikar burinsa, k'ilama *AUREN 'DAN'DANE* yayi dani, ai sainaji wani kuka ya tokaremin mak'oshi, har ina neman shid'ewa. Kamar yanda yaga sunsa ya had'a ruwa mai zafi-zafi, sannan yafito, ficewa yakumayi, babu dad'ewa sosai yadawo yakuma shigewa toilet d'in, ni dai idonama Na rufe gaba d'aya, dan bana k'aunar ganinsa. Jinai kawai an kama hannuna ana k'ok'arin tadani zaune, wata azaba naji har cikin kwalwar kaina, saina fashe dawani marayan kuka Wanda yasakashi saurin sakina nakoma Na kwanta. Runtse idonsa yayi saboda jin addu'ar danake jero masa ta neman sakayya ga ALLAH tsakanina dashi, wani bai ta6a masa makaman ciyar addu'ar nanba, amma gashi matarsa ta sunnah tana masa, duk da yasan hak'in sane ya k'ar6a agareta hakan bai hanashi jin bak'in cikiba, dan aganinsa inada hujjar masa addu'ar da tafi wannan muni, tunda Bahaka mukayi dashiba. Cikin tsantsar damuwa ya d'aukeni zuwa bayin, yayinda nikuma nake kuka ina fad'in ya saukeni, duk da a hankali nake maganar yana jina. Ba k'aramin daga mukayi dashiba wajen taimakona, harda cizonsa nayi a damtsen hannunasa, aiko yacizu wlhy, dan hakwarana saida suka huda lallausar fatarsa, (to dama ba wahala tasaniba fatar) amma a mamakina sainaga ko gezau baiyiba, kuma Na tabbata yaji zafin cizonnan, saidai bansan dalilinsa Na daurewaba, da k'yar ya samu nayi wankan tsarki kuwa, dan saida yakusa makeni ma dan haushi sannan nayi, harya dawo dani d'akin ban daina jera masa ALLAH ya isaba a fili da kiransa mugu azzalumi. Duk da kalamaina suna sukar zuciyarsa haka yadake yanuna tamkarma baya jina. Bashida maganin dasuka rubuta akan matsalata, sai dai yanada Wanda zai iya taimaka min kafin zuwa Safiya ya nemo wancan. Haka yakawo min maganin da tea wai nasha, harara kawai Na zuba masa Na maida kaina Na kwanta batareda nako motsaba balle yayi zaton zan tashi. Shima baice komaiba yakamani ya tayar, hannunsa da k'irjinsa nashiga bugu, ina kuma kaimasa cizo, amma k'arfin ba d'ayaba, bai barniba saida ya tadani, sannan ya wani ci uban Magani fusakarsa amatuk'ar murtuke, yace “kinsan ALLAH koki kar6a kokuma....humm”. Yanda yay maganar kuma sai tsoro ya kamani, Na watsa masa harara kafin nabud'e bakin, da kansa yabani shayin, sannan yabani magani. mugun Ashe harda Na barci, cikin mintuna k'alilan barci yay awon gaba dani. Sai lokacin ya samu damar sauke ajiyar zuciyarsa tareda dafe kansa dake tsananin sara masa. Duk yanda yaso yayi tunanin ya akayi hakan tafaru yakasa, saboda matsanancin ciwon da kansa kemasa, dole yamik'e zuwa d'akinsa, shima ruwan mai zafi yay wanka dashi sannan ya tsarkake jikinsa ya fito, Magani yasha ya haye gado ya kwanta shima, yasan bazan farkaba a nan kusa. Maganin barcin da shima yashane yasaka barci suresa shima. ★★★★★(())★★★★★ Tun daga shigar Muftahu wajen Galadima har zuwa sanda ya zuba Abu cikin milk d'in Galadima lokacin daya Shiga bedroom d'insa d'aukar Abu suna kallo, har ya girgiza ya ajiye kwalin da sauri inda ya d'auka, fitowar Galadima zamansa da files d'in daya bama Muftahu Na masu buk'atar taimako a asibiti da aka kawo masa zai biya, har shigowar Munaya falon Galadima da fitar Muftahu, zamanta da kar6ar wayarsa zuwa fitarta itama, yanda Galadima yafara fita hayyacinsa har dawowar Munaya sashen takawo masa wayarsa, fitarta dakuma bin bayanta dayayi, hankalinsu ne yad'an tashi ganin yadad'e bai dawoba, gakuma a yanayin daya fita. Hakanne yasaka aka turo wasu mata biyu da kayan fruits wai sukawoma Galadima domin suyi CID d'in yana ina?. Sai dai sarkin k'ofa kuma yace saiya musu iso, kamar yasani saiya rufe k'ofar ta ciki sannan yanufi sashen Galadima d'in, yayi sallama tafi sau 15 amma babu amsa, ya tabbata da yana kusa daya amsa, komawa yayi yace musu ai yamayi barci, su koma dashi kawai, babu magiyar dabasu masaba yak'i bud'e musu, dan yarigada yasan komai Na kitumurmurar gidan, sannan yasan Galadima bayacin abincin kowa a masarautar, ko ankawo su yake bamawa, idan kaga yaci abincin dawani yadafa a masarautar to tabbas aunty Mimi tana k'asar, sunzo tare kotazo ta iskeshi. dan haka yahanasu shiga, harma yad'an tsargu da tunanin kawai wani Abu a k'asa ganin sun jajurce dason shigar. Ransu a 6ace sukabar wajen, inda aka aikisu suka koma, sun Isar da abinda yafaru. Hakan kuma yakuma tada hankalin masu Aiken nasu, domin an ruguza musu plan d'insu kenan...........✍🏼 🤔hummmm.񬻹⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ _ko Yaya za'a kwashe tsakanin Galadima da Munaya da safe kuma🤣🤭, Munaya team amin afuwa🥳🙏🏻ku kora da wanan🍾🍺🍻🥂🍷🥃🍸🍹😂😝._ 🏇🏻 *_Masu karatu nasan kowa yamatsu yasan tarihin masarautar su Galadima, insha ALLAH zakuji, inason muzo ga6ar daya kamata kuji d'inne insha ALLAH, saura k'iris😄👌🏻._* Barkanmu da dawowa😄✋🏻. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣6⃣ ..........Da kuka na farka, duk da naji dad'in jikinna kuwa, dan banajin azabar kamar jiya, tashi nayi zuwa toilet danna d'auro alwala, na tuna labarin da wata k'awarmu ta ta6a bamu akan yanda taita ciwon jiki, saida mijinta yata mata ruwan zafi a ranar, ruwan mai d'an zafi na had'a na shiga ciki, nasha zafi kuma naji dad'i, amma inajina kamar ba a dai-daiba maganar gaskiya, haka dai nasamu nayi sallar asubahi, ina tsaka da sallar yashigo da nufin tadani, ganin na tashi ma saiya juya yafice abinsa zuwa masallaci shima. Koda na idar kwanciya nayi saman abin sallar nacigaba da kuka na, ina kuma tunano abinda yafaru a jiya tamkar a films ko novels ko mafarki, babu abinda zuciyata keyi sai tsinemar, a yau d'inan dolene saiya bani Sakina natafi gidanmu, nafasa auren Contract d'in ma, da dai na zauna da mugunnan gwamma nakoma gidanmu nacigaba da rayuwa dasu innaro yafimin.... Tun d'azun yana tsaye a kaina, tausayina yakamashi, dan yasan shine silar kukan mawa, bayason zalunci ko kad'an, amma saigashi shine da aikatawa kuma, zama yayi a bakin gadon, cikin muryar nan tasa mai kama da anmasa tilas yace “tashi zaune muyi magana”. “baza na masa, a zuciyata nace bazan tashiba mugu kawai, bakada abinda zaka fad'amin na yarda, azzalumi, dama abinda ka shiryawa rayuwata kenan? Dan kaganni d'iyar talakawa banida k'arfin gogayya da kai, tabbas nayi kuskuren yadda da Wanda shikansa ma bai gama yadda da kansaba, ALLAH ya Isa wlhy tunda ka ketamin mutunci har abada bazan yafe makaba, kullum cikin sallata saina sakoka da neman sakkaya ga mahaliccina akan zalincin dakami......... A fili kuma nace, “kagama zalintata kazo kanamin mazurai da mulki, ank'i tashin”. a hankali nake maganar banyi tunanin yana jinaba, sai tsawa kawai naji ya dakamin “k!!!!!”. Yafad'a cikin daka tsawa, Ashe tunda nafara maganar ya rumtse idanu saboda yanda Kalmar zaluncin suke sukarsa a zicciya, ban ta6a ganinsa a wannan yanayinba, a cikin fad'a yace, “Niba azzalumi baneba, zina nayi dakene!? dazaki dunga aibantani damun duk furucin dayazo bakinki? to bara na tuna miki idan kin manta, SADAKI na biya na auroki! tun jiya kike fad'an magana amma na shareki, ni sa'an kine? wlhy idan bakiyi wasaba zan koya miki hankali! danaso muyi magana ki saurareni mana kiji mizance?.........” Zumbur namik'e zaune, duk da azabar da k'asana kemin, na kallesa ido cikin ido ina zubda kwalla nace, “bakada abin fad'a shiyyasa bazan saurarekaba, bar ganina 'Yar talaka bana d'aukar raini wlhy, mina maka ne? miye had'ina da kai kaketa bibiyar rayuwata da bala'i, tunda na had'u da kai ban kuma samun nishad'iba, wlhy bazan yafe makab....... Jikake bamm! ya make bakina da bayan hannunsa, cikin zazzaromin ido yace bazaki nutsuba Ashe?”. Naji zafi sosai, dan haka nafashe dawani marayan kuka mai ban tausayi, ga wani bala'in tsoronsa daya kuma shigata, maganar ma a tsorace dama nayita, Dan tsabar bala'i na hango cikin idonsa Dana kallesa. Kansa ya dafe da hannu, jiyake tamkar ya tariyo jiya a rayuwarsa ya goge dukkanin abinda yafaru Ganin bazan sauraresan ba da gaske saiya tashi ya fice yabarmin d'akin. Nakuma 6arkewa da kuka. Koda yafita a falona ya zauna, ya dafe kansa daya koma masa ciwo k'asa-k'asa yau, tunaninsa yafara komawa baya daga jiya zuwa yau, shin miya sakashi wannan matsananciyar sha'awar ne wai? dan bai ta6a jin makamancin feelings irin na jiya ba, da sauri yamik'e yanufi sashensa, a falo ya tsaya, ya d'auki kwalin hollandia fresh milk d'in jiya yana dubawa, shi dai yasan shine last abu daya sha a jiya, to kenan koma miye daga cikinsa yake?. to amma ai ba yaune yafara shan fresh milk ba a gidannan balle yace kuma shine. kwalin ya ajiye yakuma dafe kansa, gaba d'aya tunaninsa ya kulle, dama shi indai yana cikin 6acinrai to komai nasa birkicewa yakeyi, dolene saiya kwantar da hankalinsa zai iya kamo bakin zaren. a kujerar Yakoma ya kwanta, ko azkar yakasayi yau, babu dad'ewa barci yakuma kwasheshi anan. Itama Munaya daga kuka barci yay awon gaba da ita a wajen. Har Samha suka kawo abinci duk barci suka Tatar sunayi, tasan halin Uncle Sam shiyasa bata tadasu ba, kad'an daga aikinsa ya mammaketa a safiyarnan. Su duka sai wajajen 12 suka farka, kowanne yatashi da damuwarsa. Tunda nayi takun farko nakuma tabbatar da akwai matsala, dan ruwan zafin da yaymin jiya kad'ai ya isa na daina jin zafinnan irin haka, balle kuma nima nayima kaina da safennan, amma maimakon k'asana yabar zafin saima zugi yake k'arawa, gashi idan nashiga ruwan, zafi nakeji sosai. Yanda nake takawar ina hawayene yabashi mamaki, dan aganinsa yakamata nasamu sukuni saboda yanda yamin jiya. bansan yashigoba, maganarsa kawai naji.. “Wai mike faruwane? Ko dai kinji ciwone?”. Wata uwar harara dataso bashi dariya na zuba masa, amma saiya danne baiyiba, takowa yayi har inda nake yakama hannuna na fisge, ya d'aure fuska shima yana hararata, “k! Wlhy kinutsu kafin na canja miki kamanni”. “yo kammani na yaushe kuma zaka canja min? bayan Wanda ka canja min yanzu? dama haka kake? a fuska kamar babu ruwanka amma sai zalunci taf zuciyarka”. Idonsa ya runtse dan bayason Kalmar zaluncin nan danake jifansa dashi, jinai kawai an fusgoni an zaunar a bakin gadon, nakuwa fashe da kuka ina fad'in “wayyo zafi, munubiya Azalumin nan zai kashe miki ni”. Ko kallona baiyiba yafice, ina nan ina kuka saigashi yadawo da wayarsa a hannu, ya zauna saman sofa batareda ya kalleninba, bashida mafita saita kiran Akash, dan yanason sanin minene matsalar datake sakani wannan kukan da complain d'in zafin, yasan koya tambayeni ba fad'a masa zanyiba.. Da turanci suka gaisa, amma da zaiyi tambayar saiya canja harshe zuwa yaren daban saniba. Akash yace saidai idan ciwo taji, dan bai kamata ace tana Complain zafi irin haka ba, zataji ciwo kam amma bawai yanda yake nuna masa yanzun ba. Galadima ya gyara zamansa sosai yace “to ai na sanar maka fyad'e akama yarinyar fa”. Akash yace “zata iya kai shekara nawa yarinyar?”. 'Dago ido yayi ya kalleni kafin ya janye yana fad'in “Maybe 19years ko 20 kawai”. “ai bama yarinya baceba can sosai, inaga taji ciwone gaskiya, yakamata doctor ya dubata gudun samun matsala, amma kabada gudunmawa a hukunta Wanda yay abunnan my man, please ka kwatarma yarinyar hak'k'inta wajen azzalumin nan”. lips d'insa kawai ya cije maganar Akash na sukar zuciyarsa, da Akash yasan shine yay aika-aikar dabai ce hakaba. sallama sukayi ya yanke wayar, saikuma yafara tunanin doctor d'in dazai nemo ya dubani, dan bashida damar fita dani a gidan yanzun. Can doctor Hafsat ta fad'o masa a rai, ita kad'ai zai iya aminta tasan matsalarsa, dan ya yarda da ita sosai, yasan zata masa k'yak'yk'yawar fahimta. Kiranta yayi bayan sun gaisa cikin mutunci ya fad'a mata matsalar ta yanda zai iya, dukda ya 6oye mata wacece keda matsalar ta fahimcesa, d'an murmushi kawai tayi tana girgiza kai da tausayin yarinyarnan data shiga hannun Galadima, duk abinda zata buk'ata tagama had'ashi sannan ta fito, matsalar gidansu data Sani yasakata yin shiri tamkar ba doctor ba. Shiru d'akin yayi, sai kukana dayake fita a hankali, shikam ya zubamin idanu yana kallona k'asan ido, zaune yake k'afa d'aya akan d'aya, ya jingina da kujera, saika rantse idonsa a rufe yake, amma yana kallonane ahaka. Bayan doctor Hafsat tazo k'ofar fada saita kirashi, dan baza'a barta kai tsaye tashigaba. Ina kallonsa ya fice bayan ya yanke wayar daban San dawa yakeyinta ba. Kusan mintun 20 saigasu sunshigo dawata mace, ba yarinya baceba can gaskiya, zasu iya zama sa'anni da Galadima d'in, dan haka na tashi zaune na gaidata cikin girmamawa. Ita kuma ta amsa cikeda fara'a. Kallon Galadima tayi dayake tsaye yana kallonmu, “ranka ya dad'a kozaka bamu wajene”. Murmushi yad'anyi yana fad'in babu damuwa. Yana fita matar ta zauna kusa dani a bakin gadon, fuskarta d'auke da murmushi tace, “sunana doctor Hafsat Abu, friend d'in Galadima ce tun a primary school”. Murmushi nayi mata na yak'e kawai. Takuma gyara zamanta tana kallona, please dear karkiji nauyina, ki fad'amin matsalarki kai tsaye, dan ba'a wasa da wannan matsalar, takan zama babban Abu anan gaba ga d'iya mace”. Kai na jinjina mata ina hawaye, sannan nace “inajin zafin wajen sosai”. “ok kozaki iya kwanciya nagani”. Ido na waro waje a tsorace, sai kuma nayi k'asa da kaina saboda kunya. Tayi murmushi tana kama hannuna, “karkiji kunya akan lafiyarki dear, please ki daure kinji”. Kai kawai na gyad'a mata sannan na kwanta, babu yanda zanyi dole na yarda ta duba, kanta kawai ta girgiza da mamakin Galadima, saikace Wanda ya kusanceni da k'arfin tuwo?, ai wannan kam da wani doctor d'inne saiya yima Galadima fad'ama wlhy, dan ko kad'an bai bini a hankaliba, amma ciwon daya jimin bazai zama mai cutarwa ba insha ALLAH. da kanta yanzu ta had'amin ruwan zafi tazuba wasu magani, sannan ta taimakamin har zuwa bayin ta nunamin yanda zanyi. ban cutar da kainaba na nutsu nayi komai yanda tace, dukda inajin zafi kuwa, bayan nafito saina sameta zaune ta gyara gadon tsaf, gakuma abinci a ajiye, da alama Galadima ne ya kawo, tsareni tayi da lallashi naci abincin ma yanzun, sannan tabani magunguna nasha, ta kalleni da murmushi, “ALLAH yak'ara lafiya gimbiyarmu, indai zaki cigaba da kulawa kamar yanda na nuna miki insha ALLAH nan da 2days zaki dawo normal, ga drugs d'inan saikina sha, shima wannan cream d'in kina matsi dashi awajen a koda yaushe”. Kaina na jinjina mata sannan nace “ nagode Aunty”. Sallama tamin tafice. A falo ta iske Galadima, bayan tamasa bayanin yanda yakamata a kula dani saita kallesa cikin tsokana, “ranka ya dad'e kafayi 6arna gaskiya, Shifa wajenan ba a nuna masa k'arfi, please a kiyaye”. Murmushi kawai yayi baice mata komaiba. rakiya yamata tareda mata alkairi sannan yadawo. A kwancen data barni ya iskeni, zama yayi gefen gadon yad'an kalleni ya janye idonsa “yaya kikeji yanzun?”. Baki na turo masa, amma ban tankaba. shima bai damu da amsawar tawaba, ya basar kawai ya d'akko wata maganar. “nasan babu abinda zan fad'a ki yarda dani tabbas, sai dai zankuma maimaita miki SAMEER BAYA ZALUNCI, koda wasa ban ta6a kawo zan aikata hakan agarekiba har kibar k'ark'ashin kulawata, bansan miya shiga kainaba a jiya”. Kallonsa nayi ina hawaye da takaicin maganarsa, nace “bakasan miya Shiga kankaba ka d'auki fresh milk kabani? bayan kasan mika zuba”. Shima kansa ya d'ago yana kallona, cikeda k'asaitarsa yace “ban fahinceki ba, mikike nufi? dan ina son na kusance ki sainayi amfani da wani abu? da hakan naso daret zanzo gareki tunda nasan nabiya sadaki ai, tunda ba tsoranki zanjiba ko?”. “dama ai bazaka fahimceni ba tunda Kasan ka aikata ai, kuma ai alk'awarin zama tamkar abokai kamin ba irin wannan ba”, na had'e hannuna alamar roko🙏🏻 ina kuka nace “dan girman ALLAH ina rok'onka kabani Sakina a yau natafi gidanmu, wlhy nafasa auren Contract d'in, koma waye yayi abun ni na yafe masama, kawai ka sallameni”. Yama rasa mizai cemin shi, ajiyar zuciya yad'an sauke, kafin ya cije lips nashi, “shikenan, zan miki yanda kikeso, amma kibari ki warke, bai kamata ki koma gida ahakaba”. ‘yana gama fad'ar haka yatashi yafice batareda yaji amsa taba. Duk da naso yabani sakina a yau, amma zanyi hak'uri na warke d'in kwana nawane. ****** Yinin yau haka mukayishi duk zukatanmu babu dad'i, Galadima kam ai ciwon mara saiya nemi dawo masa sabo, jiyayi kawai yana sake buk'atar kasancewa dani, haka yayta dannewa har zuwa dare, dan bazai kuma yarda yin gangancin nanba. ganin yana neman mutuwa yay shiri a gaggauce yafito domin zuwa hospital. Tunda yafito suke zubewa gaisheshi, hannuna kawai yake iya d'aga musu, dan kallo d'aya zaka masa ka tabbatar yanada damuwa, da sauri sarkin mota yazo yabud'e masa ya shiga, suma dogaran dakan bisa idan zai fita sai duk suka taso. Tundaga fitarsu gidan Muftahu na kallonsu, yad'an murmusa kawai abinsa. (🙄wlhy Reader's suka kamaka zaka gane bakada wayo😡) Shi kad'ai yasan azabar dayakeji a jikinsa, yana kwance cikin kujerar ne sai faman cije lips yakeyi. Tunkan sarkin mota ya tambayama ya sanar masa asibitin da zasuje. Sarkin mota ya amsa cike da girmamawa da tausayin shugabansa, dama shi tunda yaga yafito ya fahimci akwai matsala. Tun amota yakira wata number yana tambayarsa ko yana asibiti?. Dr Jalal ya amsa da eh yana nan. Yanke wayar yayi kawai baisake cewa komaiba. Dr jalal yabi wayar da kallo yana mamakin Galadima da halinsa, kiransa yakuma yi shi dan bai fahimci inda maganar tasa ta dosaba. sai dai harta yanke bai d'aukaba, yana k'ok'arin sake kira yaji ana Knocking d'in k'ofar. Amsawa yay da yes tareda izinin shigowa. Wani dogari ya bud'ema Galadima k'ofar yashiga, da hanzari Dr Jalal yamik'e yana murmushi da masa welcome. Hannu kawai ya iya d'aga masa ya zauna kujerar gaban decks d'in. Shima Dr jalal saiya zauna, “ranka ya dad'e lafiya dai ko?”. Saida yaja wasu Seconds sannan yafara ma Dr jalal bayanin damuwarsa, ya sanar masa mararsa namasa ciwo tun jiya, kuma ada bata masa kamar hakan. Shiru Dr jalal yay yana nazarin maganar tasa, saida yakai aya sannan yace “ranka yadad'e kokasha pills ne?”. Kallonsa Galadima yayi, “pills kuma? wane irin tambaya kakemin haka?”. “afuwa ranka ya dad'e, matsalar taka tayi kama da wanda yasha tablet ne, mikaci na k'arshe jiya?”. cikeda nazarin maganar Jalal yace “fresh milk ne last abinda nasha jiya da daddare”. “to amma bayan shi kafara jin matsalar?”. “kusan haka gaskiya”. Dr jalal dai shiru yayi, dan ya tabbatar wannan aikin desire tablets ne, amma koya fad'a dawuya Galadima ya yarda, sai kawai yashare ya had'a masa drugs da injection yamasa, yace yad'an kwanta na kamar 20 minutes a office d'in. bai musa masaba ya shiga inda jalal kan huta idan yaso, saiya kwanta kawai, dan shima bazai iya tafiyarba, d'akin ma da taimakon jalal d'in yashigo. Ni bansan hidimar da akeyiba, dan rabona dashi tun bayan munyi maganar saki, abinci ma tun Wanda doctor tabanine a cikina, sai kusan 8 Samha takawo min kayan fruits dawani Abu mai dad'i daban san mineneba😝. Ta zauna mund'anyi hira kafin tafice. a bakin ta nakejin wai jibi Friday zasu koma India. Na danci abinda takawo nasha magani nayi kwanciyata cikeda kewar 'Yar uwata dana kanyi akowanne dare. Galadima kam bai dawo ba sai kusan 1pm, yana shigowa sashensa yawuce yay shirin barci ya kwanta, Alhmdllh zuwa yanzu yaji k'arfin jikinsa, sai dai zuciyarsa nata cud'a masa tunanin ina yasamo pills? dan shima yafara yarda da maganar jalal, musamman idan ya tuno furucin Munaya na d'azun da safe. To kenan wani ya zuba masa bai saniba? to amma wazai zarga shikam? duk wad'anda suka shigo wajensa a jiya amintattun sane, Sauban, Samha, Harun, Muftahu, duk sun shigo wajensa a jiya, amma Muftahu shine last shigowa, shiru yay yana nazari, can kuma saiya cije lips d'insa ya lumshe idanu yana shafa gurin Dana cijesa. A haka barci ya kwasheshi. ★★★★ Munubiya tashiga damuwa sosai akan rashin jina a waya, takira number ta yafi sau goma amma switch up, gashi yaa Marwan ya hanata kiran number dana kirasu a ranar, yace wai number Galadima ce bai kamata su damesa ba. Haka taci kukanta a yinin ranar, saikace mara lafiya haka ta yini, zuwan su Ayusher ne ma yad'an sanyaya ranta har suka janye mata hankali da yawan tunani, a ranar gidan suka yini cir, sunsha hira da labarina, kowacce tana missing d'ina. Sunce suna son zuwa amma an hanasu, wai gidan danake ba gidan da ake zuwa any how bane ba, babu yanda suka iya haka suka hak'ura. ********* A gidanmu ma yau sukayi niyyar kawo min akwatinana da abinda ba'a rasaba, amma ankira wayata akashe, wannan yasa Abba yace abarni akaima su fauziyya nasu. ni daga baya idan an sameni akai min nawa d'in. Duk inda akaje da innaro ake zuwa, kowacce ta taima gidanta kallon kwaf kenan, sotake taga gidan wacce tafi acikin sauran 'yan uwana. ALLAH ya taimaki munubiya lokacin dasukaje gidanta yaa Marwan yana gidan, hakama su Ayusher. Fita yayi yasiyo musu abubuwa yakawo, sannan suka zuba musu girkin da sukayi, babu ko kunya suka mik'e kafafu suka ci abinsu, to dama gidan Fauziyya ne kawai suka samu sukaci abinci, su Safara'u kam casukai basu fara girkiba, dan ita haleematu ma ruwa wannan bata basuba, banda innarmu akaje, dayake kowacce idan za'aje gidan 'yarta banda ita ake zuwa. Zasu taho kuma yaa Marwan yabasu kud'in mota, dukda kuwa a mortar Dady yaa Anas ya kaisu. Tunda suka dawo gida aka shiga labarin yanda aka iske gidan kowa, nanfa wad'anda gidan 'ya'yansu ba'a samu wani abun kuzo aganiba sai suka fusata, kunsan dai halin jama'ar gidan namu🤣, wannan Abu saida yakawo rikici, fad'a sosai sukasha abinsu, itadai innarmu k'ala bata ceba, saima ta maida hankalinta ga girkin dare datakeyi, ga innaro sai habaici takeyi, saida gwaggo Safiyya tazo da k'yar ta lalla6ata tafita. Matan anguwa makwafta kam sun masa kunne suna saurare da kwasar dariya, dan lamarin gidanmu yazama kamar na 'yan wasan kwaikwayo. Duk tsiyar dasukeyi dady yana gidan yana jinsu, amma ko lek'owa bai yiba, danshi bashida hayaniya ko kad'an, balle daya fahimci abin yashafi 'yan bani na iya d'in gidan ne, dariya kawai yayi yace ALLAH ya k'yauta. kad'anma kenan ai, bakuga komaiba tunda yanzu kuka fara aurarwar, kuma har yanzu da sauran 6ur6ushin amarci ga yaran harsu Aunty khaleesa kam dake cikin watanni na hud'u da auren. ★★★★★ Alhmdllh yanzu kam naji dad'in jikina, dan ko ciwonma banaji, sai shirye-shiyen kayana nakeyi dan yau nakeson tuna masa batun sakina, tun shekaran jiya rabona da ganinsa, harma na d'auka baya gidan sai d'azun da safe Samha take cemin ai tare suka fita itada Uncle Sam da Sauban birnin gayu da asibiti zagayen marasa lafiya, sune har Asibitin mahaukata, tace duk atsorace take ALLAH yasa kartayi mafarki. Ni dariya ma tabani yanda take bani labarin kamar a firgice take. Komai nagama had'ashi tsaf, Galadima kawai nake jira, amma abin haushin har kusan 4pm babu labarinsa, gani nayi zan zauna jiran gawon shanu, dan haka na mik'e zuwa sashensa. Nayi sallama yafi 7 amma babu amsa, sai kawai natura na shiga, a zatona rainin wayonsane da mulkin ya motsa, babu kowa a falon sai wani k'amshi dake tashi na musamman, ko ina kuma need a gyare,, a yanda naga yanayin falon kamar babu kowa a sashen gaskiya, dan komai akashe yake har AC, dawuya kuma yana nan kaga AC n sa a kashe, duk da haka saina d'an zauna ina k'arema ko ina kallo, kai kace yau nafara shigowa, hotunansa da bana gajiya da kallo naketa kallo yanzun ma, idona nacikin zageye-zagaye saina hango wani k'aramin frame na photo, bana ganin mutanen jiki sosai dan haka namik'e tsaye, ga hoton na isa, yana a kusurwar d'akinne ta gabas, saman wani d'an katako da aka k'awata wajen, bayan foton akwai flower babba mai k'yau, sai aka jigina hoton jikin flower d'in. K'yak'yk'yawan mutum ne ajiki Wanda kallo d'aya zaka masa ka hango tsantsar kamaninsa da Galadima, saikuma mace a gefensa itama masha ALLAH, Galadima kuma yana satar kamanninsa da ita, musamman idonsa ha6arsa dawasu abubuwa, saikuma wadda nake k'yautatama zaton aunty Mimi Ce kusada matar, shima namijin ina tunanin Galadima ne, yana cinyar mutumin, bazai wuce 5 to 6 years ba a picture d'in, Anty Mimi kuma bata wuce 10 ba, sai tsohon ciki ajikin matar, dukda ban saniba sainayi tunanin iyayensane, duk cikin kayan sarauta suke. Samha ta fad'amin iyayensa suna india, Abbansa bashida lafiya, ban wani tambayeta komaiba, iyanan naji kawai. Hoton na maida na ijiye ina murmushi, sun birgeni gaskiya sosai, flower d'in nabi da kallo, itama tamin k'au, gawani k'amshi mai dad'i datakeyi, kuma nalura da dare kamar tana wuta haka. Hannuna na kai na ta6a ganye d'aya ajiki, sainaji Ashe ta roba Ce ma, mamaki ya kamani, banyi zaton ta roba bace wlhy, dan tayi k'yau. Har zan bar wajen, kamar ance na d'aga kaina saman p.o.p d'in ta jikin kusurwar sainaga tamkar CCTV camera, amma bakowa zai iya fahimtar hakanba, domin ansata cikin tsantsar kulawa, gabanane yafad'i, nayi azamar kauda idona tamkar ba ita nake kalloba, saina d'an gyara zaman flower d'in kawai nabar wajen zuciyata na tsitstsinkewa, toshi miye nawani saka CCTV camera a falonsa?, komawa nayi na zauna, zuciyata nawasu tunane-tunane daban. Sai lokacin tunanin koma bayanan yazomin, abinda Nagano ya hanani lek'a bedroom d'insa, dan nasan zai iya ganin komai ta CCTV camera d'insa. Sai kawai natashi na fice nakoma nawa d'akin.............✍🏼 Hum masu karatu kuna zaton Galadima bai fahimci Muftahu namasa zagon k'asaba kuwa🤔?. kuduba yanda ya shashantar da binciken ya akayi yasha desire tabs a fresh milk🤔. To koma dai miye kumuje zuwa, ai masu iya magana kance *Karshen alewa k'asa*🙄👎🏻. Humm ya kuke ganin sakin da Munaya ta nema? Shin zata samu? kokuwa zai bita bazai bayarba🤔?. Kumuje zuwa dai a page nagaba my guys🥳⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣7⃣ ...........A gajiye yadawo gidan, daga masarautar su papi yake, dan shine yamasa kiran gaggawa a daren jiya, yau tunda safe ya tafi, dan jirgin 7am yasamu, shine sai yanzu yake dawowa. Saman kujera ya zube yana furzo iska, sarkin mota daya biyoshi dawasu kaya ya ajiye, yana niyyar fita yajiyo maganar Galadima d'in. tsayawa yayi yajuyo yana kallonsa. idonsa a rufe yace, “kunnamin AC ”. “to ranka ya dad'e”. sarkin mota yafad'a yana risinar da kai alamun girmamawa. Ya dad'e zaune a wajen idonsa a rufe, jin ana kiran salla a masallacin masarautar yasashi mik'ewa da k'yar yanufi bedroom d'insa. makunnar fitilar ya laluba, haske ya gauraye d'akin, komai normal kamar yanda yabarsa. anutse yafara zame sky blue d'in shaddar jikinsa. wanka yashiga, bai 6ata lokaci sosai ba yafito, jikinsa ya goge tsaf yajawo jallabiya fara tas mai dogon hannu yasaka, tamasa k'yau sosai, yad'an fesa turare yafita da hanzari jin za'a tada sallar magrib. Nagaji da jiransa har zuwa magrib, bansan hawaye sun fara bin kumatuna ba, ahaka nayi sallar magrib, nayi alk'awarin ko yanzu yazo yabani sakina a gidanmu zan kwana, bayan na idar yau ko doguwar addu'a banyiba nadawo kan sofa na zauna tareda rabga tagumi na zubama akwatina idanu. A wannan yanayin yashigo ya sameni, cikeda mamaki yake bin akwatin gabana da kallo, shi yama manta dawani maganar saki da mukayi. Ban San ya shigoba saida yad'an bubbuga hanun sofa d'in, firgigit nayi ina kallonsa, bansan murmushi ya su6uce minba da ambatar Alhmdllh. Idonsa ya janye a kaina ya zauna bakin gadon “lafiya na ganki da trolley?”. Yay maganar cikin kuma d'aure face. Nikam ban damu da yanayin nasaba na rashin walwala, dan narigada na fara sabawa ma da hakan, nad'an murmusa ina ta6e baki, nace “kayan tafiya gida na had'a”. Yi yay tamkar bai jiniba ma, ya zaro wayarsa dake ring yana kallo, a mamakina sai naga yayi murmushin gefen baki tareda saka wayar a kunne. “Amincin ALLAH ya tabbata a gareki my Momma”. “tare dakai Muh'd d'ina, yakuke? Ina d'iyata?”. Murmushin yakuma yi tareda satar kallona, yace, “gata a gefena Momma, Yaya jikin Abie?”. “jiki Alhmdllh wlhy, yaushe zaku tahone? kun barmu mu kad'ai nida jakadiya”. “kai Momma duk kuyangin gidanann kice kuna cikin kad'aici?”. “to Muh'd ai d'a dabanne a zuciyar iyaye, musamman ma mu damuka k'agara muga sabuwar d'iyarmu”. Bakinsa yad'an ta6e yana murmushi, “karki damu Momma zaku ganta wataran, amma su aunty Mimi ai inaga gobe zasu taho jirgin darema suka samu”. “haka tacemin, amma kufa to? dan banjiKu a lissafin masu tahowaba?”. “nima insha ALLAH zan biyo bayansu bada dad'ewa ba Momma, dan nayi missing d'inku, bazan iya gama hutuna ananba gaskiya”. “ita kuma d'iyar tawafa?”. “nan zan barta mana Momma, duk k'arshen wata zanzo na ganta kamar yanda na saba”. “lallaikam, to yanzu dai saika nemi tickets kafin Safiya, gobe idan ALLAH ya kaimu kutaho dasu Haneefa domin takawa yaga d'iyarsa, idan kun k'are hutun tare anan zuwa k'arshen watan saika maidatan”. Tunda tafara maganar gabansa yafad'i, yawani marairaice murya tamkar yana a gabanta, “please Momma wannan shawaran kumafa? dan ALLAH karkice haka ba yanzu ba sai nan gabafa zatazo?”. “to nidai nagama magana Muh'd, za6i kuma yarage naka ai, bani ita mu gaisa time d'in gogema takawa jiki yayi zan shige”. Ransa a 6ace yamik'omin wayar, banyi magana ba na kar6a dan naji yana Momma ai nasan mahaifiyarsa ce. gakuma yanda yaketa kwantar da murya irinna ladabi da shagwa6a. Cikin nutsuwa da tsantsar girmamawa na gaisheta, daga can ta amsa min cikeda kulawa, bayanin daya firgitani naji tanamin, na waro idanu waje cikin tashin hankali, amma sai na kasa musa mata, na shiga amsawa da to cikin rawar murya. Duk da AC d'akin zufa nakeyi, nida ke shirin fecewa gidanmu yau da takardar saki amma shine ake rok'ona nayi shiri gobe zamuje India, na taresu ni Munaya, ban kuma fahimtar dukkan sauran zantukan nataba, sai maganar k'arshe naji datace nabashi wayar. Murya na rawa namata godiya da Addu'ar samun lafiya ga abban su Galadima, taji dad'i sosai kuwa, dan har sautin murmushinta ina jiyowa, hannuna har rawa yakeyi namik'a masa wayar, yana kwance idonsa a lumshe, damuwace a fuskasa karara, muryata na rawa nace, “gashi tace abaka”. Batare da yabud'e idonba ya kar6a, a kunne yasaka wayar, cikin kwantar da murya yace “haba sweet Momma na a sassautamin mana”. Murmushi kawai tayi daga can, tace “ai iya sassaucin dazan maka kenan Muh'd, gobe idan ALLAH ya kaimu ka kaita gidansu tama iyayenta sallama da 'yar uwar tagwaicinta”. “amma Momma..... ” “kasan banason maida magana baya ko? kayi yanda nace kawai”. Shiru yay bai iya cewa komaiba harta yanke wayar gaba d'aya. Ransa a6ace ya tashi zaune, wayar Harun ya kira, yana d'agawa ko gaisuwar bai amsaba yace, “Harun inason tickets guda biyu na India”. “lafiya dai ko Galadima?”. “Normal” kawai yace ya yanke wayar. Harun ya girgiza kai, dan yaji alamar ransa a 6ace yake. Mintuna basu wuce 5 ba yakirashi yace an samu naka, sai dai ita kuma batada passport ai, dolene da safe sai Anje anyo, amma na darene jirgin. “yayi” kawai yace nanma yay shiru. Harun nason masa wata tambayar amma babu dama, sai kawai ya yanke wayar. Nidai ina dafe da kai abin duniya dukya isheni, shikenan an ruguza min plan d'ina. Tashi yay yafice batareda ya kuma ko kallona ba, ban damuba, dan nima tawa ta isheni, yana fita hawayen bak'in ciki suka zubomin a fuska, ban samu damar sharewa ba na zame na kwanta a sofar. Yana fita sashen mai martaba yaje, bayan jakadiya tamasa iso yashiga, gaidashi yayi cikin saisaita yanayinsa kafin yamasa bayanin zai koma India gobe, saboda kiran gaggawa daya samu daga doctors d'in Abie. Fatan alkairi mai martaba yamasa, kafin ya tambayesa maganar nikuma fa. Kansa a k'asa yace, “ranka ya dad'e da ita zamu tafi, idan komai ya dai-daita saina maidota”. “to shine nan, hakan yayi ai” nasiha sosai mai martaba yayi masa, tareda jan doguwar addu'a wa jikin Abie, ya dad'e a can sannan yafito. ★★★★ d'ayar wayarsa daya manta a kan gadona tashiga ring, ban d'auka ba harta tsinke, aka kuma kira ta yanke, saga nan ba'a sake kiranba, tunanin kiran Munubiya ne ya zomin, Dan haka na tashi zaune ina share hawayen fuskata na d'auki wayar nasaka number, Dan na haddace ta akai, harta tsinke bata d'agaba, saida na sake kira sannan tad'aga. Acikin rashin sanin wanene tayi sallama a d'arare, amsawa nayi ina jan ajiyar zuciya, cikeda d'oki tace, “Sweetheart kece? ykk?”. “lafiya lau munu...., ke kad'aice a gidan dan ALLAH”. “eh nikad'aice yaa marwan bai dawo masallaciba. miya farune?”. “magana zamuyi Munu.... amma kiyi hak'uri da 6oye miki da nayi tun farkon matsalar, banason ki tashi hankalinkine shiyyasa” tun daga farkon maganar aurenmu da Galadima a randa suka saceni har zuwa yau ban 6oye mata komaiba, inayi ina kuka, itama daga can kukan takeyi harda shashsheka. Cikin Jan aziyar zuciya tace, “Naso nafahimci wani Abu tunkan aurenmu, amma ganin bakicemin komaiba na share, banga laifinki ba na aminta da auren yarjejeniyar kamar yanda ya buk'ata, domin kowaye a irin matsayinki abinda zaiyi kenan inhar yana tausayin iyayensa. Abu d'ayane gaskiya sai naga kamar bazai aikataba”. “mikenan?”. “Saka miki desire tabs dakikace, kiduba yanda kikace yadamu sosai, Munaya kofa saka mikin yayi babu laifi, tunda hakinsane, sadaki yabiya ya aureki, inma banda wautarki koda auren Contract d'inne kukayi ai ba'a fatar sakin ko. atunaninki innarmu wane tashin hankali zata shiga idan ance aurenki ya mutu cikin kwanaki 5 kawai da arenmu, ni yanzun shawarar dazan baki ki kwantar da hankalinki kuje India d'in, ki duba mahaifinsa, saikiga tarbar da parent nasa zasu miki, daga nan samu san mafita, idan sakin zaki nema kinga saiku rabu, idan kuma zaki iya zama da shine shikenan, saimuyita addu'ar ALLAH ya dasa masa sonki a zuciya”. “Humm, Munubiya kenan, kinga kuwa tashin hankalin danake ganowa a masarautarsun nan, wlhy akwai babban lauje cikin nad'ifa, bazan iya wannan rayuwarba gaskiya, dan tanada wahalar gaske, shi kansa ba ta6a sona zaiyiba, dan tun farko dawata manufa ya aureni ai”. Murmushi Munubiya tayi mai sauti, tace “amma ke kina sonshi?”. “ALLAH ya kiyaye, ni wlhy bana sonsa, kuma ban tunanin zansoshi ko anan gaba”. Dariya Munubiya tayi, harda kwantawa a gado, cikin dariyar take fad'in “to badai asan maci tuwoba sai miya ta k'are, kika sanima kona samu baby's d'ina a jiyan”. Kwafa nayi kawai, nace can dai a bakinki, kedai mukema fatan ALLAH yasa mun samu, ki shirya min kayan dad'i gobefa zanzo kinji Sweetheart ”. “karki damu habibati, a gaidamun Galadima ango”. tayi maganar cikeda tsokana. Aiko sai Munaya ta saka mata kuka. Dariya ta tuk'e Munubiya tayanke wayar tana mamakin yanda Munaya tayi sanyi, dawuya Munaya kaga ta zauna yima Abu kuka, koyafi k'arfinta tanada jimirin wahala, lallai Galadima baije da wasaba ashe.😆👁 Koda tayi sallar isha'i saida ta saka 'Yar uwarta a addu'a, fatanta wannan auren ko igiya d'aya karta samu rauni barema akai ga saki. ta d'au alk'awarin cigaba da sakata a addu'a a kowacce sallarta. Nima ina ajiye wayar tashi nayi nayo alwala nayi sallar isha'i d'in. Kallon hotuna na zauna yi awayarsa, duk kusan ma bawasu pictures bane na azo agani, daga hoton wayoyin salula sai na kamar kayan waya Daba a had'aba da computers, mamaki ya kamani, saikace mai k'era waya?, nidai gajiya ma nayi na ajiye wayar, har barci ya kwasheni ban kuma jin labarin Galadima ba. Shikam tunda yabaro wajen mai martaba suka fita shida sarkin mota, birnin gayu plaza yaje, yayi wasu 'yan abubuwa sannan ya gana da ma'aikatan wajen. Sai kusan around 11 ya dawo gidan, ko sashena bai kallaba ya shige d'akinsa, abinda duk zai buk'ata yad'an harhad'a, yakira Wanda zai kira awaya akan wasu harkokinsa sannan yay shirin barci ya kwanta.. Washe gari da asuba ko tadani bai zoba kamar jiya, ALLAH yasama nariga da na saba da tashi sallar tun a gidan mu, dan haka akan lokacin na tashi nayi kayana. barci nakuma komawa, ban tashiba sai 9am. Wanka nafarayi, ina tsaka da shafa mai yashigo da sallama ciki-ciki, na zawo hijjab da sauri na saka. Bakinsa ya ta6e yana kauda kai gefe. “ki shirya zamu fita”. ya juya ya fita. Da kallo na bishi ina girgiza kai, oh ni, saikace anmasa dole sai yayi maganar?. Dukda bansan inda zamuba saina d'okantu da fitar, kobabu komai nasha iska ai, danni gidannan jinsa nake tamkar wata duniya daban ba duniyarmu ta mutaneba, yo komaifa gidan akwaishi, makaranta ne asibiti k'aramine, wajen wasan yarane, babufa yanda zaka fita waje inba doleba, musammamn ma mu matan aure, garama mazan da masu fita karatu kuma. Shiri nayi cikin zani da Riga na atanfa, sunmin kau sosai, danni fa saima naga kamar fatata tawani d'an murje hakannan👁.. A falona na iskesa zaune, muka had'a ido kowa ya janye nasa cikeda basarwa, saida yagama k'asaitarsa da mulki sannan yatashi, sanye yake cikin milk d'in shadda datasha ainahin aikin masu sarauta, takalmansa ma hakanne, sai fidda k'amshin turarensa mai narkar da mutane yakeyi, sajennann ya kwanta luf bisa face nashi, hular na hannunsa bai sakaba. Gaba yayi nabisa abaya ina takuna d'ai-d'ai, takalmana masu sauk'in tsini sai bada sautin kwas-kwas sukeyi. Mun tarar da motocin dazamu fita dasu a shirye guda 3, an wankesu sai d'aukar idanu sukeyi, gaisuwar da hadiman gidan suke mana muketa kar6awa, nikam banason abunnan wlhy, amma shi ko'a jikinsa. Bud'e mana motar akayi muka shiga, nida shi muna baya, sai sarkin mota agaba, yayinda mota biyun kuma dogarai suka shiga. Babu Wanda yay magana tunda muka fita, nidai kawai kallon hanya nakeyi da mamakin ina muka dosa?, mun Isa immigration office Ashe passport za'amin, abinka da manya, cikin 1hour aka kammala min komai. Bamu bar office d'inba saida harun yazo ya kar6i passport d'in domin nema min visa, daga nan muka fito. wani dad'ine ya rufeni danaga mun doshi hanyar gidan mu, shi kansa ya hango farin cikin dake shinfid'e a face d'ina, ya janye idonsa daga kallona ya maida kan kallon mutanen anguwar daketa hada-hadarsu hankali kwance. A dai-dai k'ofar gidanmu motocin suka paka, da hanzari na nemi 6alle murfin zan fita. Caraf ya damk'e hannuna, juyowa nayi ina kallonsa tamkar zanyi kuka, idonsa a lumshe yake tamkar ma baisan miyayiba. “dan ALLAH ka sakar min hannu naje”. ‘nayi maganar tamkar zanyi kuka’. Banza yamin, saida yamula dan kamsa sannan yabud'e idonsa a kaina yana hararata, “ki nutsufa, ko an fad'a miki haka akeyi?”. Baki na tunzuro gaba. Ya janye idonsa daga kallona yana kuma matse hannuna cikin nasa. Ni ban saniba Ashe wai dole sai an nema masa ison shiga gidan namu, sarkin mota dai tuni yafita dama. 'Yan anguwarmu sunyi cirko-cirko suna kallon motocin, jira kawai suke suga Wanda zai fito aciki, dukda sunga masu jajayen riguna a tsaitsaye, alamar daga masarauta ne. Muna a haka saiga yaa hameed yafito daga cikin gidanmu dad'an hanzarinsa, inaga yazo gaidasune, dan kullum Safiya duk sai sunzo shidasu yaa Shafi'u. Jikin motar damuke ya k'araso, sarkin k'ofa yay knocking d'in glass d'in 6angaren Galadima. duk da yasan yana kallonsu shi. Sauke glass d'in yayi a hankali, sannan yama sarkin k'ofa nuni daya bud'esa, har yanzu hannuna yana cikin nasa kuma. Ya d'auki hularsa ya saka. Cikeda fara'a Yaa Hameed yake masa barka da zuwa, sai lokacin ya saki hannuna, sannan yazura k'afarsa d'aya yafito, nima dogari d'aya yazagayo da sauri yabud'emin, na fito, handbag d'in hannuna dogarin ya kar6a yana zubomin kirari. Kallofa Yakoma sama ga 'yan anguwarmu, kowa sai kallona yake yana fad'in ashe munaya Ce, kai masha ALLAH, kugafa auren sati d'aya harta canja kamanni, lallai sarauta dad'i. Inda yaa Hameed da Galadima suke na zagayo, suna rik'e da hannun juna sunyi musabaha, fuskar yaa Hameed a washe, yayinda ta Galadima ke d'ukeda wani munafukin murmushi. Cikin murna nace “yaa Hameed I miss u”. “miss u too Darling sister. bismilla ranka ya dad'e kumuje ciki to”. Atare muka shiga ciki, ina gaba suna bina a baya shida yaa Hameed. Matan gidanmu kowacce na mak'ale jikin window d'inta tanason ganin Galadima, yayinda Aryaan da Aiyaan suka shek'o da gudu kaina, ganin haka suma sauran yaran sai suka shek'o, duk na tarbesu cikeda farinciki da kewa. Ni nama manta dawani Galadima muke tare, Ashe shi yanata kallonmu cikeda sha'awa. yaa Hameed yamasa jagora zuwa falon Dady. Nikam ai d'akin Innarmu sha, tareda gayyar 'yan tarbata. A zaune na iske innarmu tana ninke kayan su Aryaan, da alama wankewa tayi, sai tausayinta ya kamani, yanzufa kowanne aiki dole itace zatakeyi, babu mai tayata, jikinta na fad'a ina hawaye. Itakam tace “kajimin ja'irar yarinya, to miye abin kukan kuma? wai nikam yaushe kika lalace da sauri kuka haka Munaya?”. “innarmu kewarku cefa wlhy”. nashiga gaidata, cikeda farincikin yanda na koma a kwana 6 kacal take amsamin, sai jero hamdala take a zuciyarta. Zainab k'anwar Fauziyya tashigo d'auke da tire an d'oro zo6o da ruwa akai. “inyee, kaga su zee anzama 'yan matafa, kace bad'i sai aure kenan?”. Fuskarta ta rufe tana fad'in kai Aunty kibari please, innarmu kice ta daina”. Innarmu dariya take mana itakam, saiga Rahma itama tashigo, saiga Ameenatu da Khadija ma, lallai bad'ima Ashe zamu aurar da yawa, a kwana ki 6 d'innan sainaga yaran duk sunmin girma a ido. Nasha mamakin su na zuwa gaisheni, dan bansa akaba nikam, araina nace ko jama'ar gidanmu dun fara canja haline dai?. Muna haka saiga innaro tamkar an jehota, kowa ido ya zuba mata, dan shigowa tayi tana masifar wai bamu fara shiga gidan taba nida Galadima. Na kalleta a d'age ina ta6e baki, “yo banda abinki innaro ai sai nafara ganin Uwata, dan banida kamarta kaf duniya”. Ha6a tarik'e tana kallona “eh lallai kam, yo ai Dama ke halin uwarki gareki, ba mutuncine dakeba, ballan tana yanzun kuma ido yak'ara fetsarewa ansan komai na aure”. Zan maida mata murtani innarmu ta harareni, shiru nayi na k'yaleta badan nasoba. Shima Galadima yana falon Dady yasamu tarbar mutunci daga maman Fauziyya, dan matan gidanmu babu wadda ta aika masa dako ruwa, yaji dad'in tarbar daya samu kuwa, musamman yanda su Abba suka nuna masa tamkar d'ansu, baiyi dubi da sarautar dake kansaba ya duk'a har k'asa yakwashi gaisuwa wajen iyayena uku. Hakan yamusu dad'i, domin ya mutuntasu, kuma sun kuma tabbatarwa shid'in mai tarbiyyane. Anan yamusu bayanin munzo musu sallama ne zamu tafi India. Fatan alkairi su abbanmu sukai mana da k'yak'k'yawar addu'a, daga nan sukad'an ta6a hira dashi, dukda yana nonnok'ewa saboda kunya irin ta jinin hausa Fulani. Nikam can innarmu ta iza k'eyata nashiga kowanne d'aki na gaidasu, sai kallon k'urulla suke bina dashi, anason ganin wata makusa a jikina, amma sai basuganiba kuwa, komai sai sambarka. Aikam bak'in ciki tamkar ya karsu, kowa hassada nacin zuciyarsu (kai jama'a ALLAH yarabamu da cutar hassada komai k'ank'artatta😢🙏🏻) Na dad'e d'akin maman Fauziyya sosai, dan acanma naci abinda tad'an girka mana mara nauyi, yaa Hameed yazo ya d'auki na Galadima da kansa. Sashenmu na dawo inatama innarmu shagwa6a, duk nabi na nanik'e mata, dukda tureni datakeyi. Nashiga tsohon d'akinmu harda kukana, komai nanan yanda yake, harma dawasu 'yan tarkacenmu daba a gama badawa ba, haka kawai bamu mutuba d'akinmu Yakoma kango, anan na d'akko cajata da wayar Galadima daya barmin a filin idi, sai wad'ansu 'yan abubuwa danake buk'ata. Na fito ina tambayar innarmu waye ya d'auki wani hotonmu dake saman mirror nida Munaya?, tacemin maybe Ameeran inna lami Ce ko Bilkisu, dan taji suna rigima akan d'aukar Horton. Shigowar Galadima da yaa Hameed tasaka innarmu yin shiru, nikam ban daina daddaga k'afa k'asaba ina k'unk'unin miyasa tabari suka d'auka?. Galadima dake k'ok'arin zama yad'ago ido yad'an kalleni sannan ya janye. Yaa Hameed ne yace kekuma lafiya?. Fad'a masa nayi tamkar zanyi kuka, yace “to kuka zakiyi?”. “ALLAH yaa Hameed inason hotonfa”. “ai saiki hak'ura yanzun tunda sun d'auka ko?”. Innarmu da Galadima dai gaisuwa sukeyi, babu Wanda ya tanka mani. shi saima mamakin ta6arar danakeyi yake a zuciyarsa. Nikam bansan yana yiba. Sosai yaji innarmu ta burgesa, yakula ko kad'an ba halinta nabiyoba, dan ita tanada sanyi, dagani batada hayaniya, amma nikam ai sai addu'a. Yad'an jima anan dukda ba hira sukeba, kowa kunya na cinsa, a raina nace dama yanda kunya guy d'inan ashe?. Alkairi mai yawa ya ajiyema innarmu, dawata leda da yaa Hameed yabiyosa da ita, sannan yafita innarmu na saka masa albarka yana amsawa cikeda jin dad'i, jinta yake tamkar Momma d'insa. Daga nan saida yashiga kowanne d'aki, sannan yaa Hameed ya rakashi gidan innaro. Abba ne yashigo yana fad'in a tattaro lefena muwuce da kayanmu. Na marairaice fuska nace Abba abarsu anan, kagaba tafiya zamuyi can d'in babu kowa. “a'a Munaya bazai yuwuba, idan mun ajiyesu anan mizamuyi dasu?, kitafi da kayanki, duk randa dai kuka dawo suna d'akinki ai. Badan nasoba na amince, amma naje wajen kayan ina fitar da wasu, ni saima yau naga lefen, gaskiya su Galadima sun zuba kud'i a wajennan. Duk matan gidanmu atanfofi na fidda musu, maman fauziyya kam guda biyu, sannan yaran gidanmu 'yan matan yanzu kowa nafidda masa wani abun, su Aryaan ma dukda mazane kowa na fidda masa abinda zai iya amfani dashi. Sai su Ayusher da inna lami da Ameera, Bilkeesu ma da nata, hakama mama rabia, na ware akwati guda na lodama Munubiya kaya sosai aciki, aunty salamah ma da nata, sai gwaggo Safiyya da yaranta mata, itama innaro jarabatu na fidda mata, su Abbanmu ne dai narasa mizan basu aciki. Innarmu na kira tagani, ta kalleni tana fad'in “munaya bazasuga an kwashe kayanba?”. “a'a wlhy innarmu bazasu ganiba, kowafa da sashensa a gidan, kuma babu mai shiga harkar wani, idan na barsu mizanyi dasu? Kayan sunmin yawa ai”. “to shikenan, ALLAH ya saka da alkairi”. Na amsa da ameen ina fad'in “ganaku nan keda su Aiyaan innarmu”. “a'a ni bazan d'auki komaiba, bakiga yama kawomin abuba, ga kud'i dama bansan ko nawa bane”. Kuka na Sanya mata akan saita kar6a, babu yanda ta iya ta amsa, amma saida tarage. Sai dai tana fita na maida mata harda k'arima. Zainab Ce ta kaima kowa nasa, kowacce rai babu dad'i ta amsa, sotayi ace daga 'ya'yantane wannan abun arzik'in yafito bawai innarmu ba, (basusan shi Ubangiji babu ruwansaba, yakan azurta Wanda yaso Yakuma k'ask'antar da Wanda yaso a lokacin dayaso). Babu wadda tazo godiya sai maman fauziyya, nace “oho dai, aikin banza wai talaka ya girmi sarki🤷🏻‍♀”. Banyi maganar su d'auki motarba, dan sonake nasami cikon d'ayar nabasu su duka ukun. Nima naje na gaida innaro, dasu Abbanmu, naje gidan innaro lokacin su Galadima harsun fito,, na iske Ashe gwaggo Safiyya tama koma jiya, sai d'iyarta Habiba datake zawarci aka bari anan. Munsha hira da ita, tanata yaba k'yan da nayi. Innaro kam dukda jana datake ajiki sai basar da ita nakeyi, amma hakan bai hanata yaba Galadima ba, catake wai na more miji, nafi kowa morewa a gidanmu. Nidai banda ta6e mata baki da bak'ar magana babu abinda nakeyi, bata damuba saboda neman gindin zama take ajikina. Bamu baro gidanmu ba sai gab daza'a shiga sallar juma'a, an taho da motata da lefena, duk kayan daza'a bana mutane kuma na barsu a can, harna Munubiya. Su Abba sunsha alkairi awajen Galadima Ashe, hakama matan gidanmu d'akin kowacce daya shiga saida ya ajiye alkairi, sunata kukan zuci da fad'in inama-inama 'ya'yansu ne a wannan daular🤣🥴. Zamu shiga motane ina sharar kwalla baba k'arami yace namusu godiya wajen Galadima, kaina kawai na iya d'aga masa. Innarmu bayan tafiyarmu har 'yan kwalla tayi, matan gidanmu kam duk haushinta sukeji, idan kacire maman fauziyya. Daga nan gidan Munubiya muka nufa, amma anan bai shigaba, yace naje zuwa anjima zai dawo mutafi, dan yanzu zaije sallar juma'a. Kai na kawai na d'aga masa, nafita bayan dogari d'aya yabud'emin k'ofa, basu bar gate d'inba saida sukaga na shige ciki, ya maida kansa jikin kujera ya kwantar tareda lumshe ido, abinda yafaru a gidanmu kawai yake tariyowa, yakula family nawama sai a hankali dai. Sunada shigen irin halallayyar family d'insa. Nikam da gudu nashiga ina kwala kiran sunan Munubiya, itama yafito aguje muka rungume juna, sai muka fashe da kuka kawai, ALLAH ma ya somu yaa Marwan yarigada yafita masallaci.................✍🏼 *_Masoya bansan yanda zan nuna muku tsantsar farin cikinaba, amma tabbas inajin dad'in Comments naku, kuyi hak'uri da rashin amsawata d'ai-d'ai, kunmin yawane wlhy, ga massages na PC, idan kuma nagama typing d'inan kaina d'aukar zafi yake, ko son ta6a waya banayi wlhy, naga wasu suna d'auka kamar wulak'ancine rashin amsawar, wlhy ba haka bane, kumin afuwa da uzuri please & please, duk da nasan bazan iya k'yautatama kowa acikinku yanda yakamata ba, dole wani yaga gazawata koyayane tawani fannin😄._* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_* *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣8⃣ ...........Bansan yanda zan musalta muku farin cikin damuka tsinci kanmuba nida 'yar uwata Munubiya, abin kawai ba'a magana. Duk da bata yarda zan zo d'inba amma bata fasa tanadar min duk abinda tasan inasoba, tarasa inda zata sakani dan dad'i, gaskiya gidan munu yayi k'yau sosai, gashi an cika ko ina da kaya, kasancewar harda nawa aka had'a mata, muna yin salla muka 6arke da hirar yaushe gamo, a haka yaa marwan yazo ya samemu, yaukam abin mamaki naga fara'a a fuskarsa, nace lallai aure yayi citta kenan, yanda yake bama Munubiya kulawa sai abin ya birgeni, kamar Na lashesu kuwa Dan dad'i. Haka muka yini muna tad'i har lokacin sallar la'asar yafita salla. A lokacinne aunty Salamah tazo gidan, Ashe Munubiya ce takirata ta fad'a mata zamu tafi India yau da daddare, mun tarbeta da murna sosai, yayinda ita kuma taketa yaba wai munyi k'yau. mukaita rufe fuska alamar kunya. Shawarwari taita bamu akan rayuwar aure da yanda zamu tattali mazanmu, babu ko kunya take 6aro mana komai, sai mune muketa sunkuy da kai, itakam ko a jikinta, ta rarraba mana wasu buks da ke d'auke da abubuwa masu amfani dazasu bada gudunmawa a zaman takewar aure, nidai bawai na d'auki nawa da muhimmanci baneba. Wajen 5 tatafi, tafiyarta babu dad'ewa saiga Galadima da yaa marwan sun shigo, Ashe wai ya dad'e a k'ofar gida zaune, ya kira yaa marwan yace baya gida amma gashinan zuwa. Shine yajirashi amota harya iso suka shigo tare. Sun gaisa da Munubiya a mutunce, ta shirya musu abinci, da yace yagode sauri yakeyi, amma munu ta marairaice wai yaza'ayi mijin 'Yar uwarta yak'i cin abincin gidanta, in baimasa baneba ta sake masa. Murmushi yayi ya zauna yaci kad'an, yayinda mukuma muka shiga d'aki dan mu basu waje suci abincin, d'an kuskus d'inmu mukayi muma, takuma kwantar min da hankali akan auren nawa da wasu 'yan shawarwari, da nunamin fushinta akan abinda nace nama Galadima d'in, ta nunamin wannan ba tarbiyyar da iyayenmu suka bamu baneba, gaskiya karna sake irin haka, kuma nabashi hak'uri akan hakan, nace “to amma tayaya zan basa hakurin?”. 'Yar takarda ta d'auka tayi rubutun tabani wai nabashi. Na kar6ane kawai badan ina tunanin zan bayar d'inba, duk da nasiharta ta shigine gaskiya, kuma nima tun a ranar nayi nadamar ce masa azzalumin gaskiya, Duk da nasan a cikin fushine Nima Na fad'a, Dan nashiga rud'ani sosai akan abinda yayimin daban zataba. tabani kayan da aunty salamah takawo a Leda, batareda na dubaba na amsa. Itama k'yauta mai tsoka yamata sannan muka fito, nida ita kowa yana sharar kwalla, bamason rabuwa da juna, amma yazamuyi? aure ya rabamu. Daga nan gz yaa marwan muka nufa gaida mama rabi'a, namayi mamakin yanda yasanta, nankam tare muka shiga, su Ayusher suka rukunkumeni cikin tsantsar farinciki da kewa. Bamu dad'e sosaiba itama ya ajiye mata alkairi muka fito, su Feena ma yabasu kud'i wai su sai kayan kwalliya, hakama Ahmad, yaa Fadeel dai mun tarar baya nan, yakoma inda yake bautar k'asa. Nanma saida nayi kuka dazamu taho. Saida muka shiga mota ina sharar hawaye sannan ya kalleni cikeda k'asaita yana ta6e baki, “ke wai bak'ya tsoron hawayenki su k'are ne?”. Bance masa komaiba nacigaba da kukana, shima saiya shareni. ★★★***★★★ Koda muka isa Masarauta bamu wuce sashenmu kai tsaye ba, wasu 6angarorin gidan mukaje mukai musu sallama, harda sashen mama Fulani, yauma dai babu magana mai dad'i tsakaninta da Galadima, nifa lamarin nasu na d'aure kaina gaskiya. Mai martaba kam munsha addu'a a wajensa, sannan muka fito. Mun shiga sashenmu ana kiran sallar magriba, zan shige yace “kiyi azamar shirya kayanki trolley d'aya, karki wani kwashi kaya dayawa”. Da to kawai na amsa nayi shigewata ciki. *_7:30pm_* Muka bar masarautar, nida shi da Samha motarmu d'aya, muna baya tana gaba. d'ayar motar kuma Sauban da aunty Mimi da khaleel ne aciki. Mun sami rakkiyar Harun da Muftahu sai wasu k'alilan daga masarautar. Tom nidai ba k'auyace a airport, dan banta6a shiga jirgiba, amma kunsan mutuniyar taku da Jan aji,🤨 saina Fiske abina nima inajan citta tamkar wadda ta saba. Duk abinda yadace ayi anyi mana, musamman ma ni danake sabuwar fita k'asar, harun yad'an sha cukuniya a kaina tunda rana. 9pm dai-dai jirginmu ya shilla a gajimare😆😜🛫. Lokacin da akace asaka belt ban sakaba, sai shine ya jawo yasakamin batareda yace uffanba, yana jikin window nikuma ina gefensa, sai bayan mu khaleel da Samha, can baya kuma aunty Mimi da Sauban. Ina lafe jikin kujera, yayinda shima yake kwance ya jingina bayansa, wani English novel ne a hannunsa yana karantawa, dama tun amota yake rik'e da kayansa. Da akazo tambayarmu mi muke buk'ata Coffee kawai yace yacigaba da karatunsa, nima ta tambayeni saina girgiza mata kai alamar bana buk'atar komai. Janye book d'in yayi yana kallona, saikuma ya janye ya maida kanta, harta bar wajen ya kirata, yace takawo min abinda su Samha sukace sunaso. Bance komaiba nidai, shima saiya cigaba da karatunsa. (*************) Alhmdllh mun sauka kasar India, k'asar da nake gani a films, abin mamaki sainaga dogarawa ne sukazo tarbarmu, saikuma Akash dawani danaji Galadima yakira da beejay. Bamu 6ata lokaciba mukabar airport d'in, a nawa tunanin sainaga rayuwar tasu kamar dai tamuce gaskiya, saidai banbancin sutura zuwa wasu mu'amullat haka, mutane sunata hidimarsu da kai kawo hankali kwance. Masha ALLAH na fad'a yayinda muka isa gidan danake k'yautata zaton nasu Galadima ne. gidan kam yamin k'yau gaskiya, su beejay basu shigaba suna saukemu suka juya, mune muka Shiga hannuna aunty Mimi tarik'e, yayinda su Samha suke agaba. Galadima kam mun barsa a harabar gidan yana waya. Ai kaina bai gama kwancewa ba saida muka shiga falon gidan, hummm manyan k'asarmu sunajin dad'insu gaskiya, yo kanada irin wannan gidan a k'asar daba takaba to k'asarka kumafa?. A falo muka zube bayi suka Shiga hidima damu, muna zaune a wajen Galadima yashigo, shima zaman yayi ya aza k'afa d'aya bisa d'aya, Sauban yazuba ruwa a cup yabashi, kar6a yay yana fad'in “thanks”. Ya kalli baiwar datake shirya abinci daga can gefenmu, “k zonan”. Da sairi ta ajiye spoons d'in hannunta tanufo inda muke, agabansa ta zube tace “gani ranka ya dad'e”. “kisamu wata ta tayaki Ku gyara d'akin can nakusada Samha yanzun nan”. “angama ranka ya dad'e”. tayi maganar cikeda tdantsar ladabi. Aunty Mimi Na najinsa batace uffanba. Shigowar momma tasaka khaleel tashi da gudu yaje ya tarbota, itama Samha zuwata ta kwakwameta, tunkan ma afad'amin nagane mahaifiyarsu Galadima ce, koda yanda fuskar kowannensu ta washe da farincikin ganin juna. Hankalinta Na kaina tana murmushi da fad'in “oyoyo d'iyata”. Zamowa nayi daga kujerar na durk'usa har k'asa ina gaisheta, ta k'araso inda nake ta kama hannuna ta tadani nakoma saman kujerar, “zauna kinji, sannunku da zuwa, kinsha hanya ko?”. Murmushi nayi ina duk'ar da kaina. Galadima yace “wai Momma dan ALLAH duk baki ganmu baneba?”. Kallonsa tayi cikin Hararar wasa, tace, “yo naganku bata taku nakeba”. Su aunty Mimi dariya suka Sanya, yayinda Galadima yad'an 6ata rai yana fad'in “da tsohuwar Zuma dai ake Magani Momma”. “a fad'arka ba, amma sabuwa ma aitafi aiki da dad'i”. Nidai murmushi nakeyi, Dan wasan nasu ya burgeni, inason ganin family haka cikin farinciki, gaskiya sai sunfi jin dad'in zaman nan fiyema da masarautar sun can. Gaishe-gaishe aka shigayi, kowa yana k'ok'arin bama Momma labarin yanda biki ya kasance, sai dad'i takeji da sanya albarka, nidai nida Galadima babu mai cewa komai. Mik'ewa Galadima yayi, “bara nad'an watsa ruwa Momma”. “to afito lafiya Muh'd”. ta kalleni nima, “d'iyata tashi kibi mijinki kiyi wanka kuzo ga abinci”. Harya fara tafiya saiya tsaya, juyiwa yayi yana mata magana a yaren daban saniba. Ta galla masa harara da masa dak'uwa, itama bansan mitace masaba. naga dai ya tura baki yaci gaba da tafiyarsa. ita kuma tace natashi naje. (Wai ashe cayay mata ai yasa a gyaramin d'akin da zan zauna, shine tamasa dak'uwa tana cewa d'akin safa?, shi idan ance Araba mana d'aki saiya amince?, to tare zamu zauna, shine yakuma cewa ammafa d'akinsa ai ba kowa ke shigaba, tace tasani aii, muje nima sirrinsace ai, shinefa ya tura baki gaba). Kamar an maken k'afafu haka nabisa abaya muna taka steps d'in benen, har muka isa k'aramin falo mai k'yau, komai farine a wajen, TV ce kawai takasance bak'a. Falon yad'anyi k'ura alamun ba'a gyaraba (babu mai aikin dake hawa samansa, gashi kuma sunyi tafiya suduka, Momma kuma batada time d'in gyara masa d'aki). Guntun tsaki yaja yana yamutsa fuska, d'an zaman danayi dashi na fuskanci bayason k'azanta komin k'ank'antar datti yata yamutse fuka kenan, bamu tsaya ananba muka shiga bedroom d'in bayan yabud'e, mayataccen k'amshinsa yana manne da d'akin, sai dai nan d'inma yayi k'ura, waya yazaro yayi kira, ashe Samha yakira, yace “k zoki gyaramin d'aki”. Bai jira cewarta ba ya yanke wayar. Bance masa uffanba nima nataka nawucesa, bina yayi da kallo dan yaga ina zanje?. Zanin gadon na yaye duka, nacire rigar filaluwan tareda rumfar da akama gadon, shidai kallona kawai yakeyi, yana tsaye jingine da bango (baiyi tunanin zance zan gyaraba). Knocking d'in da akayine yabada izinin shigowa, Samha ce d'auke da kayan tsintsiya, ta zubesu a k'asa tana fad'in “aunty kibarsa zan gyara”. Kaina na girgiza nace “barshi Samha, nunamin kawai yanda zanyi, kije kema ki huta”. Nunamin komai tayi, har inda bedsheets suke, tafice a d'arare da zaton Galadima zai hanata yace takoma ta gyara. Amma saitaji baice komaiba, yama kauda kansa gefe kamar baisan munayiba. Bathroom nashiga, nazage sosai na tsaftaceshi, Dana k'urarce kawai, duk abinda zaisa toilet k'amshi da tsafta nasakashi, saida naganshi need sannan nafito, ban iskeshi a d'akinba, Dan haka hankali kwance Nagyara bedroom d'inma nagama, nasaka kamshi sosai. falon nafito danufi gyarawa, sainaga Samha harta gama itama tana saka air fresheners masu dad'in k'amshi, da turaren wuta irin namu na gargajiya. Sannu da aiki namata, itama tamin, Galadima yafito daga wata k'ofa yawucemu batareda ya tankaba, bedroom d'in yakoma. Kallon Samha nayi nace, “saura wannan d'akin daya fito cikin ko?”. “ai Aunty wannan d'akin dakansa yake gyarawa, babu mai shigarsa duk gidannan inba Momma da Mummy na da shiba”. Cikin mamaki nace “miya sa to?”. “d'akin sirrinsa ne aunty”. Ban fahimci maganarba, bankuma tambayeta ba, ta tattara kayan damukayi amfani dasu tafice tana fad'in “aunty bara naje nayi wanka, dama wankan zanyi yakirani”. Kaina kawai na iya d'aga mata, saman kujerar na zauna shiru ina nazarin maganarta, miye kuma ma'anar d'akin sirri? nashiga k'ololuwar nazari banyi zaton time yawuce hakaba, k'afata yad'an shura, nad'ago idona ad'an firgice na kallesa, haryayi wankan yana sanye cikin jajayen kaya na Adidas, sun masa k'yau sosai. Juyawa yay zai sauka k'asa yana fad'in “kitashi kije kiyi wanka”. Bai jira cewata ba ya sauka. Nima saina tashi nayi yanda yace, d'akinsa sosai ya had'u gaskiya, harma bansan Yaya zan fasalta mukuba, nasan farin Abu namai tsaftane, lallai yanada tsafta, daga bedroom parlour zuwa bathroom nashi komai farine, bedroom d'inne kawai keda d'an sirkin Golden kad'an-kad'an shima. Nidai ina wanka da d'unbin tunani, haka kawai naji kwad'ayin son Shiga d'akin sirrin nasa. Koda na fito saina saka zani da riga na atanfa, ban shafa komaiba na d'auki turarensa na saka saboda neman magana😂. ina tsaka da saka turaren Samha tashigo kirana. Ajiyewa nayi na d'auki gyale nabi bayanta. Falon k'asa muka sakko, inda aka shirya abincin saman wata lallausar darduma, duk suna a zaune har Momma, kusada Galadima daketa cin abincinsa ko kallon mutane bayayi Aunty Mimi ta nunamin wai na zauna. Kamar nafasa kuka haka naji, Sauban dake gefen haggunsa yace, “auntynmu har yanzu amarcin bai k'are bane? kin shige d'aki kinyi bulum”. Murmushi kawai nayi na k'asa ce masa komai, dan yabani kunya gaskiya, nakula kuma yanada yawan tsokana, aunty Mimi kam dariya tayi, yayinda Samha tarufe baki tanayin tata. Momma tamasa dak'uwa, “o kai Sauban ALLAH ya shiryeka, kowama bazaka d'agama k'afaba?”. Dariya ya kumayi yana satar kallon Galadima dayay tamkar baya wajen, yace “to ai gaskiya nafad'a Momma. dan ALLAH aunty ba haka bane?”. “gaskiyarka fa Sauban”. Aunty Mimi ta fad'a tana dariya. Momma tace “barsu kinji my daughter, ci abincinki”. Kai na jinjina mata cikeda kunya. Galadima dai har yanzu baice k'alaba, baima d'ago ya kallemu ba. Haka muka ci abincin nidai duk a takure nake, kamar yanda yafara cin abinci haka yarigamu kammalawa, tashi yay yabar wajen, yakoma can saman wasu kujeru guda biyu ya zauna, laptop d'in dake saman table d'in wajen ya d'auka ya kunna, da alama shiya ajiye kayansa. Bayan mun gama duk muka mik'e, kowa ya hau shirin zuwa asibiti duba Abie, time d'in barcin sane shiyyasa ma Momma tasamu tataho, jakadiya kawai aka bari a wajen, itama a waje, da yake in time d'in barcinsa yayi kowa fitowa yake daga d'akin a barsa shi kad'ai. Galadima saboda aikin da yakeyi yace muyi gaba shima zai taho. Momma tace “to matarka ta zauna ta jiraka, mudai mun tafi”. Kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru, cigaba yayi da aikinsa harsuka fice, jinai kamar nace nidai zan bisu kawai. Amma na makaro, dan harma sun fice abinsu. Ganinai tsayuwa ta isheni, shikuma d'an latsin baice na zauna ba, sai kawai naje na zauna d'ayar kujerar dake kallon tasa, nima na d'ora k'afa d'aya kan d'aya tamkar yanda yayi. nayi gefe da kaina cikin basarwa. Daina danna System d'in yayi, ya d'ago idanu yana kallona, yayinda yake Murza hannunsa na haggu daya d'ora guywar a hannun kujera hannun yana sama, yinai tamkarma bansan yana kallona ba kwata-kwata. cije lips d'insa yayi kad'an, ya janye idonsa ya maida ga system d'in, aransa yana mamakin izzar yarinyarnan, tabbas data fito gidan sarauta da anga mulkin tsiya. Falon shiru babu kowa, tunda kuyangin suka gama hidimarsu duk suka koma 6angarensu dake can baya. Kusan mintuna 40 yagama abinda yakeyi, laptop d'in ya kashe sannan ya mik'e, batare da ya kalleni ba yace “muje”. Saida na d'an ja wasu seconds sannan na mik'e, saidama ya juyo ya kalleni, dan har yakai k'ofar fita. Gyalena na maida saman kai nabiyo bayansa, a k'ofa na iskeshi tsaye, na fito shikuma ya daddana wasu madannai agefen k'ofar, Ashe wai security yasaka. Ranar farko danaga yayi tuk'i da kansa, dogarin dasuke gate suka bud'e mana muka fice. Tunda muka tafi ba Wanda yayma wani magana, shi yanata deriving d'insa nikam ina kalle-kalle abuna, mun Isa katafaren asibiti mai k'yawun gaske, inma badan sunanba da saika d'auka wani wajen shak'atawa ne, asibitin ya had'u gaskiya, har ciki muka shiga bayan security sun mana 'yan tambayoyi dakuma gaisawa da sukayi, naga alamar sun sanshi sosai, amma duk da haka saida akai searching d'inmu. Abin ya birgeni gaskiya, inda aka tanada domin parking ya tsaya, ya kashe motar sannan muka fito kusan a atare, bai tafiba saida na zagayo, muka jera zuwa ciki, yanata gaisuwa da jama'a, ina mamakin yanda ya iya yarurrukansu, nikam dai saidai da turanci nake gaishesu, kuma ba kowaba. Mun fara zuwa office d'in wani doctor, suka d'an tattauna akan cigaban da aka samu na jikin Abie, mun gaisa dashi yaymana murnar aure, murmushi kawai nayi, sai Galadima ne ya amsa masa. Daga nan muka shiga d'akin da Abie yake jiyya, iyalansa su aunty Mimi duk suna zagaye dashi, nidai a raina danaga d'akin nace oni kamar ba Asibitiba?. Tunda muka shigo fuskar dattijon dake kwance a gadon ta fad'ad'a da murmushi, kallo d'aya namasa naga kamanninsa dana hoton d'akin Galadima na Nigeria. Gabansa muka k'arasa, Galadima ya durk'usa yarik'o hannunsa, nima saina durk'usa ina gaidashi da Hausa. Momma ce tazo ta kamani na tashi, cikin wani yanayi tace, “d'iyata ai Abban naku baya iya magana kinji”. Da sauri na kallesa, ya sakarmin murmushi, sai kawai na mayar masa hawaye nabin kumatuna domin tausayi, duk kallona sukeyi sukam, harda Galadima. Kuma zamewa nayi na durk'usa a gaban gadon, cikin rawar murya nafara jera masa addu'ar samun sauk'i wajen ubangiji. duk suna amsamin da amin. Murmushi yakasa barin face d'in dattijon, Wanda k'aunata take shigarsa har zuciyarsa, Momma takuma d'agoni a karo na biyu ta rungume tana lallashina. Galadima ya had'iye hawayen dake Neman zubo masa shima, yafara gaida Abie dake murmushi, da ido ya nuna masani wai ya lallasheni mana. Sai Galadima yayi murmushin jin kunya yana susar k'eya. Murmushi Abie yayi sosai, har hakwaransa na bayyana. Ban ta6a jin tausayin Galadima ba sai yau, dama haka suke cikin tashin hankali? Lallai dan ba'aga dariya a fuskarsa ba ba laifi baneba, nama yabama k'ok'arinsa yanda yake zirga-zirga tsakanin Nigeria da nan d'in. Ahaka akaita firar dani bana fahimta, danshi Abie da idanu yake maganar. Bamu baro asibitinba sai dare sosai, a can mukayi salloli dacin abinci. Mun taho muka baro Momma a can, jakadiya ma ta biyomu, dama Momma kad'ai ke kwana a wajensa, shima ba kullumba, dan wasu ranakun basa bari a kwana dashi, a sati sau uku take kwana a wajensa. ********** Tunda muka baro asibitin tsohonnan ketamin yawo a zuciya da ruhi, sai cud'awa nake da kwancewa, inason jin labarin masarautar su Galadima gaskiya. Yanzun ma iza k'eyarmu aunty Mimi tayi muka wuce d'akinsa, muna zuwa bathroom yashiga, kusan mintina 25 saigashi yafito, da Alama wanka yayi, harya sauyo kayan barci aciki, dama da abinsa yashiga. Nima tashi nayi nashiga da nawa masu kauri a hannu. Wankan nayi da shirin barci, sannan nasako hijjab na fito. Saman gado na iskeshi yawani barbaje a tsakiya, alamar baya buk'atar wani ya hau. Na ta6e bakina, a raina nace koma bakayi hakaba ai bazan ta6a had'a makwanci da kaiba, aikin banza kawai, naja tsaki a zuciyata. Saman sofar d'akin na hau na kwanta, inata tunanin Abie da ma tsalarsa. Kasa daurewa nayi, na kallesa nace, “ wai miye matsalar Abie (kamar yanda naji suna fad'a)”. Shiru yamin, harma na zata yayi barci, sai can yacemin “ciwone dai kawai”. daga haka yaja bakinsa yay shiru. Nima shirin nayi, dan bakuma nida abin fad'a, musamman yanda yabani amsar. Nidai zan iya cewa barcina na daren ranar rabi da rabine, kewar 'yan uwana da bak'unta, gakuma matsalar babansu Galadima data k'asa Barin zuciyata. Da asuba narigashi tashima, na fito toilet bayan gama d'aura alwala na iskeshi zaune bakin gado dafe da kai, k'ala bance masaba nad'au abin salla na shinfid'a, tashi yayi ya shiga bayin yana Jan tsaki a zuciyarsa, Shifa wlhy dukya takura, yasaba zamansa shikad'ai a d'akinsa, yanzu duk anzo an cika masa🙄. Haryaje k'ofar toilet d'in yadawo baya, doguwar riga ya d'auka ya shige, saida yay wanka da brush sannan yayo alwala yafito sanye cikin jallabiya blue. Turare yad'an fesa sannan ya d'au key d'in mota yafita, Ashe inda yake zuwa sallan can gaban gidanne, kuma daga sallar asuba yake wucewa asibiti ya kar6i Momma tataho gida itakuma, duk ranar weekend haka yakeyi, yanzu kuwa yana cikin hutune. Da yake ina sallah yafita, banyi zaton yafita kenanba, bayan na idar saina d'an kwanta, maganar d'akin sirrinsa ce taita cin zuciyata, namik'e nafita, saida na lek'a falon k'asa naga babu kowa sannan nadawo, cikin tantama na murd'a k'ofar d'akin, sai naga ta bud'e, banyi zaton hakaba gaskiya, musamman danaji an kira d'akin dana sirri. (bakisan ya manta bane bai rufeba Munaya😆 dan harda security a d'akin). 'Dakin k'aramine bashida wani girma, gaba d'aya bangon d'akin zagaye yake da hotuna, sai Computers guda hud'u da kuje d'aya gabanta akwai deck's babba, wanda duk Computers d'in akansa suke, sai pens da yawa cikin wani d'an Abu, gefe kuma k'aramar loka Ce ta glass cikeda takardu, gakuma tarin wasu takardun kashi-kashi da akayi kamar files a seman decks d'in, matsawa nayi jikin bangon nafara kallon picture's d'in, hotunan mutanene daban-daban, harda wasu manya dana Sani a TV, mafi yawa yayi rubutu a k'asan kowanne photo, bana fahimtar rubutun gaskiya, danhaka nacigaba da kallon picture's d'in kawai, harda na mama Fulani,😂 😱 Kutu melesi hotona fa jama'a a d'akin sirri, naga idi, nakaranta rubuntun k'asan yafi sau goma ban fahimci komaiba, saiwasu lissafi-lissafi kamar mai rubutun Mathematics😫. Na Muftahu nagani a k'arshe, abinfa ya d'aure minkai, mu kuma ni da amininsa Muftahu miya kawomu d'akin sirri🙆🏻?. Agogon d'akin na kalla naga 7am tayi, da sauri nafita gudun karya zo ya sameni. Na rufe k'ofar a hankali nakoma bedroom d'insa, ajiyar zuciyata na sauke ganin bai dawoba. Zama nayi na zabga tagumi ina tunanin ma'anar wad'ancan pictures d'in dana gani, danma a tsorace nake, ban nutsu tsaf naganiba🤦🏻‍♀. Ban sauka k'asaba saida 9am tayi agogon k'asar, na iske su Samha suna breakfast, harda Momma, na durk'usa har k'asa na gaidasu itada aunty Mimi, cikeda fara'a suka amsa. Momma tace “ai nayi zaton barci kike, shiyyasa na hana a tadoki”. Cikeda kunya nace “a'a na tashi tun d'azun”. Aunty Mimi ta zaunar dani kusada ita, Sauban ya had'omin komai na breakfast d'in. Yanzun ma a kunyace naci abincin, kunyata na burge Momma sosai. Bayan mun kammalane Momma ta kama hannuna muka shiga d'akin ta, a bakin gado ta zaunar dani itama ta zauna, anutse ta kira sunana. Hakan yasani maida hankalina a kanta nima dan nakula magana mai muhimmanci zamuyi da ita............✍🏼 *_tofa, mi Momma zata fad'ama Munaya kuma?._*🤔 *_Ya ALLAH ka gafartama Iyayenmu😭🙏🏻_* *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻2⃣9⃣ ...........“Munaya taimakona nakeson kiyi akan mijinki”. 'Dagowa nayi na kalleta cikin tsantsar mamaki, saina sinne kaina alamar jin kunyar ta, nace “Umarni zaki bami Momma, domin ke mahaifiyatace”. Murmushin jin dad'i tayi kamfin takamo hannuna cikin nata, “Alhmdllh Munaya, nagode da wannan karamci naki, yanzu nakuma aminta Muh'd yasamu irin macen danake musu addu'a shida d'an uwansa, ALLAH yayi miki albarka. nasan dukkanin yanda aurenku ya gudana”. Gabana yafad'i, a raina nace badai Na yarjejeniyar ba?.......maganarta ta katsemin tunanin. “Mahaifina Sarki Abdul'fatah shine yasakashi aurenki saboda abinda yafaru daku, Wanda nasan k'addarar Muh'd ce kawai tashigo dake cikin lamarin. Kafin nafara neman alfarmar zan fara baki tarihin masarautar su Muh'd, da dalilin zamanmu wannan k'asar daba tamuba tsawon shekara 24 kenan”. Kaina na jin jina mata, nace “to Momma”. Zamanta ta gyara sosai yanda zataji dad'in fad'ar abinda ke a bakinta. *_MASARAUTAR GAGARA BADAU A WASU SHEKARU DASUKA SHU'DE🤔_* Masarautar gagara badau masarautace mai d'unbin tarihi, da mulkinta ya gudana hannun sarakuna masu yawa, a hasashen masana masarautar sarakuna a k'ala 51 ne suka mulketa harda Sarki na yanzu, wato *Sarki jalaludden Abubakar*. Sunan masarautar awani shud'ad'd'en lokaci ba *gagara badau* ake kirantaba. Tasamo sunan gagara badaune dalilin wani Sarki daya mulki masarautar a zamani mai shud'ewa. Abaya mulkin masarautar basai ka mutuba yake barin hannunka, a'a, da zarar anyi yak'i kayi sakakin da aka ci masarautar tom dolenefa kayi murabus a nad'a wani kuma. kuma bawai cikin 'ya'yankaba, saidai asamo wani hazik'i a masarautar a nad'ashi sarautar. Tom alokacin Sarki Hameesu Alasan sai aka kawowa masarautar wani gagarumin hari dayaso girgizata. Sarki Hameesu yanada wani d'a da ake kira da suna *Barde* amma asalin sunansa shine Salisu. lokacin da aka kawo musu harinnan ba'a cikin shiri sukeba, amma haka Salisu barde yay saurin had'a mayak'a suka tunkari wannan runduna, bak'aramin gumurzu akashaba, sojojin masarautar Sarki Hameesu duk sun salwanta, amma hakan bai tsorata Salisu ba, yacigaba da bata kashi shida wasu 'yan tsirarun mayak'a, ALLAH mai iko saigasu sunci wannan runduna data kawo musu hari. Wannan nasara da Salisu yasamuce tasaka babansa Sarki hameesu sauka a kujerarsa aka nad'a salisu. tundaga ranar takoma *_MASARAUTAR GAGARA BADAU_* abin nufi annan salisu barde yazama gagara badau. Bayan Sarki Salisu gagara badau sarakuna kusan goma sunyi mulki kafin Sarki *_ABUBAKAR_* kakansu Muh'd kenan, mahaifin su takawa. Shima ya gaji sarautarne a hannun mahaifinsa Yusufa. Rana d'aya aka nad'a Abubakar Sarki shida amininsa d'an sarkin kan karofi yarima Abdul'fatah, mahaifin Abubakar Yusufu abokine ga Sarki idres na ll, dan haka rana d'aya suka yanke shawarar yin murabus suka nad'a 'ya'yansu. Sannan aka d'aura musu aure kuma a ranar da matan da su Sarki Yusufu & Idres suka za6a musu. Gimbiya Marawuyya (mama Fulani) d'iyace ga waziri Sama'ila k'anin Sarki idris, a masarautar Idrees kenan, Sarki idres bashida d'iya mace, dan haka ya d'auki mama Fulani d'iyar k'aninsa yabama Abubakar d'an Sarki Yusufu a masarautar gagara badau, shikuma Sarki Yusufu ya d'auki Khadeeja (inno) yabama Abdul'fatah d'an Sarki idres. To Ashe ita gimbiya Marayuyya (mama fulani) tana masifar son yarima Abdul'fatah ne, kuma yasani, amma ya nuna mata shi dama gimbiya Khadija (inno) k'anwar abokinsa Abubakar yakeso. Tun daga lokacin gimbiya Marayuyya (mama Fulani) ta tsani Khadija (inno), ko wani Abu yahad'a masarautunsu bata mata magana, sai zagi da habaici. Sukuma iyaye basusan gimbiya Marayuyya nason yarima Abdul'fatah ba, sukayi wannan had'in aure. (Iyayen mama Fulani ma sunso ta Auri yarima Abdul'fatah d'in domin sarauta ta dawo tasu) Gidan sarauta idan an shata layi babu mai k'etarashi, dan haka gimbiya Marayuyya da iyayen ta dolen suka hak'ura da auren yarima Abubakar (tunda acanma suna saka ran gadar sarautar) haka aka kawota gagara badau. ita kuma Khadija (inno) aka kaita masarautar su Mama fulani. Kusan atare duk suka haihu, saidai Khadija (inno) namiji ta Haifa, yayinda Marayuyya (mama Fulani) ta Haifa mace. Duk da ba masarauta d'aya sukeba hakan yasaka mama Fulani bak'in ciki, dan aganinta inno taje zata gaje musu masarauta, ita kuma bata samu damar gaje tasuba. A haihuwa ta biyu kuma sai inno ta Haifa mace, mama Fulani kuma ta Haifa namiji. Alokacin kuma duk mazajen nasu suka k'ara aure, daga Sarki Abubakar har Sarki Abdul'fatah. kamar atsare haka sukaita kuma aure har suka cika mata hurhud'u. A masarautar gagara badau Mama Fulani na zuba mulkinta a masarautar, yanda kasan itace sarkin, dayake shi Sarki Abubakar yanada hak'uri da sauk'in kai. Humm matan Sarki Abubakar duk basu haihuba, sai mama Fulani keta zubo 'ya'ya. Saikuma amaryar Sarki ta uku ta Haifa d'anta namiji, kusan tare da mama Fulani a haihuwa ta hud'u, duk da mama Fulani itace da manyan 'ya'ya mace 1 maza 2 hakan bai hanata shiga tashin hankaliba, saita shiga tsangwamar gimbiya bagobura da aibanta d'anta *Saifudden*, wani lokacin har shegantashi tayi, saida Sarki Abdul'fatah yazo har masarautar ya taka mata birki sannan. Mama Fulani tasaka sauran matan Sarki Abubakar sun juyama gimbiya bagobura baya gaba d'aya, batada sakewa ko kad'an acikin gidan. Sarki Abubakar yasan komai dake faruwa a gidansa, amma saiyayi tamkar bai ganiba, bakuma Dan mama Fulani tafi k'arfinsa baneba, yadai zuba mata idanu kawai yaga iya gudun ruwanta. Ahaka yaran suka taso, gimbiya bagobura ma bata sake haihuwa ba, sai mama Fulani ce takuma biyu, mace 1 da autanta namiji Hayatudden. Saifudden da jalaludden sun tashine tamkar tagwaye, dukda Saifudden ya girmi jalaludden d'in dakusan 1½ kuwa. danma mama Fulani na hana jalaludden sakewa da Saifudden ne. Kokuma Kamaludden da Shamsudeen suyita dukan Saifudden idan sun gansa tareda jalaludden d'in. Ahaka Saifudden yatashi cikinsu a tsangwame har suka girma suka zama manya. Saikuma wani Abu tashin hankali ya samu, a time d'in da mama Fulani ke ganin sarauta zata dawo wajen 'ya'yanta sai ubangiji ya nuna mata ikonsa. Dan kuwa Shamsudeen da kamaludden sai sukayi had'arin jirgi zasuje umara duk suka rasu. A time d'in a marine kawai ba a saka mama Fulani ba, amma hauka tuburan tafara a masarautar gagara badau. Saida aka had'a da addu'a sannan talafa, saita kullaci gimbiya bagobura, wai ita tama 'ya'yanta asiri suka mutu domin d'anta Saifudden yagaji sarauta. Gimbiya bagobura zata tada hankalinta Sarki Abubakar yace tama kwantar da hankalinta. Bayan mutuwar su Kamaludden babu dad'ewa aka had'a auren gimbiya Zakiyya d'iyar Sarki Abdul'fatah da Saifudden aure, shikuma lokacin Jalaludden da Rafi'atu d'iyar wani Sarki. Aikam sai mama Fulani ta hau bala'i wai munafunci aka shirya. Babu Wanda yabi takanta akasha biki. Gimbiya Zakiyya da gimbiya Rafi'atu kusan atare suka haihu a time d'in, gimbiya Zakkiya ta Haifa d'iyarta mace, saidai tana haihuwarta ko ganinta batayiba takoma ga ALLAH😭. Wannan shine silar aurena dana Saifudden. Dan bayan rasuwar yayata gimbiya Zakiyya da kwana 7 aka d'aura min aure da yarima Saifudden, domin nacigaba da rainon abinda tabari. Banason Yarima Saifudden, domin ina masa kallon *Mijin yayata* amma banida yanda zanyi, dole na aminta da auren domin yima iyayena biyyaya. Nasha wahalar zama dashi, saboda shi hankalinsa yana kan yayata ne marigayiya, silar soyayyar danake nunama Habeefa (aunty Mimi) d'iyar da gimbiya Zakiyya tabarine ya siyamin soyayyar yarima Saifudden, a hankali har shak'uwa tafara shiga tsakanina dashi. Soyayar dayakema 'Yar uwata saita dawo kaina. Sai daifa inashan wahalar mama Fulani, duk da kuwa itad'in (Gwaggona ce) tana amsa sunan k'anwar mahaifina, amma k'iyayyar datakema mahaifiyarmu gimbiya Khadija (inno) saita shafemu, duk da abaya tana ik'irarin son mahaifinmu Sarki Abdul'fatah kuwa. Kamar yanda yayata gimbiya Zakiyya tasha wahalarta a gidan nima hakane, saima tawa taso fin ta 'Yar uwata, bansan dalilintaba, wai Ashe dan ina tsananin kama da inno ne😆. “Ina fata dai kina fahimtata Munaya” ‘Momma tayi maganar tana kallona dana rabga tagumi inajin cakwakiyar masarauta. Kaina na jinjina mata cikin damuwa. Saitayi murmushi tacigaba da fad'in. Mama Fulani taso d'iayarta ta farko gimbiya Mansura ta auri yayanmu yarima Abubakar, Wanda babanmu Sarki Abdul'fatah yayma amininsa takwara. To saikuma hakan bata faruba, dan ita tata dabarar itada iyayenta, idan Yayana Yarima Abubakar ya auri gimbiya Mansura sarauta takoma hannunsu kenan, tunda yarima Abubakar shine magajin masarautar mu, kinga ai d'ansa ne zai gajesa kenan, idan tahad'a auren kuwa yazama jikanatane da masarautar nan gaba. To saikuma tsarin nata bai yuwuba, saima nida yayata mukazo masarautar gagara badau tushen mahaifiyarmu mukayi kane-kane, gashi kowa yana Saran Saifudden shine zai gaji masarautar gagara badau alokacin, tunda manyan 'ya'yan Sarki Abubakar sun rasu, Saifudden kuma shine babba namiji a lokacin. Shiyyasa takuma d'aukar karantsana ta d'aura mana muda gimbiya bagobura. Bayan haihuwar Haneefa babu dad'ewa gimbiya bagobura ta rasu, rasuwar data gigita yarima Saifudden kenan da Sarki Abubakar har ma da jama'ar masarautar gagara badau, amma banda mama Fulani da sauran matan Sarki, dansu hakanma dad'i yamusu. Sanadin rasuwar gimbiya bagobura Sarki Abubakar ya kwanta ciwo, sai yayi murabus yace a d'aura d'ansa Saifudden a madadinsa. Wannan Abu yama kowa dad'i a masarautar, amma banda mama Fulani dakejin tamkar tamutu dan bak'in ciki. Saidai batada yanda ta iya, tanaji tana gani yarima Saifudden yazama Sarkin masarautar gagara badau. Alokacinne kuma akace dole ya k'ara aure, dan Sarki baya zama da mace d'aya, gashi kuma ni ban haihuba har lokacin. A rana d'aya aka d'aurama Sarki Saifudden aure da mata biyu. Nanfa mama Fulani tashiga jansu ajiki wai dan a kuntatamin, tana kuma koya musu yanda zasu kuntatama shi Kansa Saifudden d'in. Sarki Saifudden nada shekara 9 a karagar mulki ALLAH yayma Sarki Abubakar rasuwa, mutuwarnan ta girgiza mahaifinmu Sarki Abdul'fatah sosai, dan saida aka had'a masa a addu'a. Tun daga wannan lokacin masarautar gagara badau takoma hannun mama Fulani, dan sai yanda tace tanaso Sarki Saifudden zaiyi, dayake shi mutumne mai sanyin hali, baya ta6a sa6a mata. Duk da haka wannan bai ishetaba, hattada yanda za'a gudanar da mulki saita tsara. Har lokacin amaren Sarki Saifudden babu wacce ta haihu. Cikin ikon ALLAH sai gani da ciki, babu kitumurmurar daba aima cikinnan nawaba d'anya zube amma ALLAH ya k'addara mijinki *Muhammad Sameer* saiyazo duniya. Lokacin Dana haihu shekarar haneef 10 cif a duniya. Muhammad shine jika namiji na farko da aka fara haihuwa a masarautar gagara badau, dan kuwa matar Jalaludden ma mata taketa haihuwa. Daga nan nima ban sakeba saida Muhammad yacika shekara hud'u, yanda Saifudden yasha tsangwamar mama Fulani haka Muhammad ma yashata tun yana yaro. Shima Sameer hak'urin mahaifinsa Saifudden ya gado sosai, dan ko abu aka masa saidai yayi kukansa ya goge hawaye, koni bazai sanarmawa ba, saidai in wata baiwa tagani ko Haneefa (aunty Mimi) su sanarnin. Da *Ciwon zuciya* na haifi Sameer, dan haka kullum cikin kaffa-kaffa muke dashi saboda gudun samun matsala ga lafiyarsa, da yawa jama'ar gidan sukan masa abune wai dan zuciyarsa ta buga💔 ya mutu. sun manta rayuwa da mutuwa duk Na ALLAH ne. Da sauri na kallo momma. Ta d'aga min kai tana murmushin takaici, “hakane d'iyata, kullum burinsu kenan akan Muhammad tun yana yaro.. Ranar wata litinin da asuba Sarki Saifudden yafita sallar asubahi sai kawo manashi akayi cikin gida, wai yafad'i ana tsaka da sallah. A lokacin kafafunsa ne kawai basa aiki, amma sauran jikinsa yana motsawa. Nice naita wahalar jinyarsa, ga cikina yafara tsufa, sai jakadiya ke taimakona, amma sauran matan Sarki ko'a jikinsu. A hankali ciwo yacigaba da girmama a jikin takawa, tun ana kafa har yadawo duka jiki, idonsane kurum ke aiki a lokacin. A asibitin garinan muke jiyyarsa a time d'in, a asirce batareda jama'ar gari sun saniba. Acikin wannan tashin hankalin na haihu Namiji, shine Abubakar (Sauban). Nidai lokacin kawai ina rainon Sauban ne, amma rabi duk Haneefa ce (aunty Mimi) yayinda kulawar Sameer takoma hannun k'anwata Zaituna (mom), autarmu kenan, dan dole aka dawo da ita wajena tana taimakamin. Na haifi Sauban babu dad'ewa aka maida sarautar Saifudden akan Jalaludden d'an gidan mama Fulani, saikuma lokacin jama'ar gari suka San Sarki Saifudden bashida lafiya ma. Ko kad'an ban damuba, danni ta lafiyar mijina nakeyi ma. A lokacin anta kananun magana akan zargin mama Fulani dawasu kuma manyan attajirai, dan akwai wani zaman sirri da sarki Saifudden yayi dawasu attajiran k'asar ana jibi abin zai sameshi, kuma anga yafito ransa a 6ace daga tattaunawar, alamar sun buk'aci wani Abu ya hanasu kenan. suma angansu ran nasu A 6acen. Nikam bamma maida hankali akan wannanba, mahaifina Sarki Abdul'fatah shine kawai tsaye akan ciwon Saifudden, saini kuma da jakadiya. Masarautar kuwa ai duniya sabuwa. Matan Sarki Saifudden ma duk sun kama gabansu, sunce bazasu iyaba. Shekararmu d'aya a asibiti babu wani canji, saima jikinsa dake neman fara ru6ewa saboda komai sai an masa. Baya iya d'aga koda d'an yatsane. (Tun farko likitocinmu na nan sun Sanar damu an masa allurar gubane, kuma guba mai had'ari, dan babu makarinta, itakuma tana sakar da jijiyoyin jikine su daina aiki gaba d'aya, wannan yasaka jikin Sarki Saifudden ya sandare😭. Wani amintaccen likitanmune yabada shawarar mu maidashi India dansu sunada kwararrun likitoci, kuma zaifi samun kulawa da tsaro a can. Wannan shine silar dawowarmu wannan k'asa, da cuku-cukun mahaifina Sarki Abdul'fatah, dan komai namu mukam ya k'are, duk abinda Sarki Saifudden kedashi yagama k'arewa a neman Magani. Tunda muka dawo India kuwa Sarki Saifudden yafara samun kulawa ta musamman, saidaifa maganar ta kud'ine. Wasu sarakuna da yawa sun bamu gudunmawa, wasuma suna akan bamu. Sanin Zara bata barin dami, gashi kullum cikin buk'atar kud'i muke sai mahaifina yakafa wasu sana'oi da sauran kud'enmu, tanan muke samun kud'in shiga. Karatun Muh'd da Haneefa kuma Mahaifiana ke d'aukar nauyi.. Tundaga primary har jami'a anan Sameer yayi karatunsa. Kiyayyar Saifudden kuma ga mama Fulani saita dawo jlkan Muh'd gaba d'aya, kokad'an bata k'aunar ganinsa, kullum tsakaninta dashi sai aibantawa da jifansa da kalamai masu had'ari ga yaro. Tunda Muh'd yafara sanin Kansa, yaga halin da mahaifinsa yake saiya fara canjawa daga mai hakuri zuwa mai zafi. Ga ciwonsa kuma, duk yabi yayta kuntata zuciyarsa akan ciwon mahaifinsa da burin d'aukar fansa. Muh'd mai fara'a da barkwanci yakoma mutum marason magana da azabar rashin d'aukar raini, duk da hakurinsa nanan bai dainaba, dan zakata masa Abu ya shareka kamar bai ganiba, sai randa yazo k'arshene zaka gane kurenka a wajensa. Mahaifina Sarki Abdul'fatah shine yamatsa tun Muh'd na secondary school dole idan akayi Hutu yazo najeria, dan acewarsa tahakane kawai zai fahimci sarautar gidansu. Muh'd ya karanci Engineering ne, dama tun yana yaro kingansa kullum cikin son had'a Abu yake, shine tsinka wayar fitila tsinka ta redio ya had'a wani abun, tunma ina masa fad'a harna bari kawai. Ashe abincinsa awajen yake. Yanzu haka sunada Company na had'a wayoyi📱 da Computers💻🖥, da sauran kayayyaki dai. Sannan yana wasu business domin dai muke samun kud'ad'en kulawa da mahaifisa da sauran matsalolinmu, dan babu mai kulawa damu a masarautar gagara badau sai Sarki Jalaludden. Wani zuwa da Muh'd yayi Nigeria shine aka bashi sarautar *Galadima*, galadima Sarautace mai k'arfin gaske, dan sai d'a mafi soyuwa ga Sarki ko k'ani ake bamawa. Kuma akance batada banbanci da sarautar waziri, dan duk abinda waziri zaiyi Galadima ma zai iyayinsa. Akwai ma wasu abubuwan da daga Sarki sai Galadima kan yisu a fada. Da da farko nace ya mayar musu amma sai mahaifina yace a'a, ai hakan da sukayi dai-daine. Sharrin kuwa dakika sun masa, har tsautsayi ya jefaki a ciki, sunyine dan hankalinsa ya tashi, har takai zuciyarsa ta buga ya mutu sun huta. Dan ayanzu ne suke ganin sunfa *kashe macijine basu sare kansaba* Galadima yazamar musu *RAINA KAMA.....*, basuyi tunanin zaikai tsawon rai hakaba, saboda Ciwo mai had'ari dake a tare dashi. Shikuma Muh'd yafi karkata hankalinsa ga jama'ar wajene sukama mahaifisa haka, koda akwai jama'ar masarautar gagara badau to kalilanne, kuma mama Fulani kawai yake zargi. Nikuma ba ita kad'ai nake zargiba, amma yakasa fahimtata gaba d'aya har kawo yanzun kuwa. Dagashi har Haneefa sunfi zargin jama'ar waje, don mutananen masarautar suna 6oye musu ainahin fuskarsu ta zalunci, mama Fulani ce kawai tata take a bayyane. Wannan yasaka tun sharrin da akai muku nasaka amin bincike a kanki, Alhmdllh ban samu wata matsalaba a tarihinki,, daga nan na dukufa addu'a da neman za6in ALLAH. bamma kai ga furtama kowa matsalata ba sai mahaifina Sarki Abdul'fatah (papi) yace Muh'd saiya aureki. Nasan ba sonsa kikeba, amma ina rok'on ubangiji da yasa wataran kuso junanku, kinada tarbiyya da wayon da zaki iya canjamin Muh'd, dan banason hallayarsa ta yanzu, nafi son nake ganin walwala atare dashi a ko yaushe, ki taimakeni ki shiga rayuwarsa sosai, dan ke macece, sai kin fishi zama cikin jama'ar masarautarsu, zakuma ki fishi fahimtar halayyarsu, sannan kidinga bashi shawara akan abinda yadace dashi. Inaji a jikina zaki iya canjamin Muh'd, saboda kinada hankali. gudun kar wani yasakama zuciyarki tunani daban yasaka nace yakawoki da wuri, domin kisan yanda zaki rayu a masarautar, kafin kutafi insha ALLAH komai Na zamantakewar masarauta za'a koyar dake kinji”. Kaina Na gyad'a mata, sannan a sanyaye nace “Momma namiki alk'awarin zai taimakesa akan matsalarnan, kuma zan bama rayuwarsa gudun mawa insha ALLAH, Sai dai Abu d'aya ne ban ganeba”. “miye baki ganeba d'iyata?”. “Abokinsa Muftahu, shima a masarautar yake?”. Murmushi Momma tayi, tace “daga Muftahu har Harun duk 'yan masarautar ne, Muftahu kakanni suka had'a dasu Muhammad, da kakan Muftahu da Sarki Abubakar kakansu Muh'd uwarsu d'aya ubansu d'aya, shikuma Harun d'an waziri ne na yanzu, kuma shima wazirin haifaffen gidanne, saidai inason sanin ko wani Abu kika gani tareda wani acikinsu?”. Kaina Na girgiza alamar A'a. Momma ta sauke ajiyar zuciya, “Munaya saikin dage kinji, domin Na had'aki da aiki mai wahalar gaske, mai kuma sark'akiya, musanman akan halayyar Muh'd, dan bai yarda da kowaba dakike ganinsa nan, koyaya Abu ya had'aku sai yayi zargin turoka akayi garesa, kuma zaka Shiga jerin wad'an da yake tuhuma. amma kekad'aice mafi kusanci da Muh'd yanzu, zakifi kowa sanin matsalarsa da wuri, saikuma kin fimu fuskantar tunaninsa, danni kinga jinyar mahaifinsa tasa banwani zauna dasu irin sosai d'innanba, yanzu haka kafin nasan matsalarsa 'Yar uwata Zaitun (mom) tasani ko Haneefa (aunty Mimi), garama Sauban. Nace “shikenan Momma ki tayamu da addu'a kawai”. “insha ALLAH muna kan yimuku kullum, ALLAH yayimuku albarka, ya albarkaci aurenku da dukkan rayuwarku da abinda zaku haifa”. Ban iya amsawa ba, kaina Na k'asa nikam, ko azuciya ma ban amsaba, dan nayi alk'awarin zai taimakesa kamar yanda ta buk'ata. Amma ina gamawa zan nemi sakina, koda nanda shekaru 2 ne kuwa, amma gaskiya Na tausayama Galadima, dan nakula yana cikin tsakkiyar mak'iyane masu fuska biyu. abinda kuma nalura da Momma bata ganeba shine Galadima bawai bai yarda 'yan gidansu nada saka hannu akan ciwon babansa bane, baya dai nunawane kawai, sai dai bansan dalilinsaba. CCTV camera d'in dana gani a d'akinsace tadawomin a rai, maybe ya sakatane domin sanin masu shiga da fita koda bayanan. Haka Na kusan yini cikin damuwa da tausayinsa, dan duk saiya bani tausayi wlhy. shiyyasa zaka gansa kullum shiru-shiru, gaskiya 6angaren hak'uri Na yarda yanada hak'uri kam. *********** Yau saida yamma mukaje muka duba Abie, mun iske Galadima baya asibitin, dama tun da rana yazo gida yay wanka yakuma fita. Har dare muna a asibitin, saida Galadima yazo muka taho tare, ina gaba ni da shi da khaleel dake barci a cinyata, yayinda sauban da aunty Mimi da Samha ke baya. Maganar da samha ta fad'amin d'azun a asibiti ta dawomin a rai, Ashe mahaifinsu ya rasu suma shekara 2 kenan, itace d'iyar Aunty Mimi ta farko, sai Hakim da suka rasu tareda babansu, saikuma khaleel auta. Suma a Nigeria da suke zaune, bayan rasuwar mahaifin nasune suka dawo nan india, duk da dangin mahaifinsu sunso kar6arsu papi yahana, babansu tsohon Governor ne shima, mutuwar tasa kuma akwai lauje cikin nad'i shima, dan ya tsananta akan binciken ciwon surukinsa Abie sosai, shiyyasama ake zargin an kasheshine saboda wani Abu daya gani. Har muka Isa gida bansan hirar dasukeba a baya, dan shima Galadima baya cewa uffan. Shine ya kar6i khaleel a hannuna, ya sa6ashi a kafad'a muka shiga ciki, har d'akinsa ya kaisa. ni lokacinma harna haye saman..........✍🏼 Barkanku da juma'a. Zanyi last page gobe idan ALLAH ya kaimu da rai da lafiya⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Network yanata min iskanci tun jiya shiyyasa kuka jini shiru☹ *_YA ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻 *_Typing📲_* *_HASKE WRITERS ASSO...💡_* _(Home of expert and perfect writer's)_ *_♦RAINA KAMA......!!♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* 👉🏻3⃣0⃣ ..................Da sallama ciki-ciki ya shigo, nayi saurin maida zip d'in rigata sama nafasa cirewa, a sace ya kalleni yawuce bakin gadon ya zaune tareda dafe kansa. Kallonsa nayi Na kauda idona nima, kusan mintuna 3 kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa. d'agowa yayi yakuma kallona, kamar an masa dole yake maganar cikeda k'asaita, “k! Wai bazakima Momma magana ba kikoma d'akinki?”. Kamar bazanyi maganaba saikuma nayi batare da Na kallesaba, “inaga kaine yakamata kamata maganar ai, dan nima zanfi son haka, duk nabi Na takura zama da Namiji d'aki d'aya”. Banza yamin bai sake tankawa ba, saima yamik'e yana jan k'aramin tsaki, nikam Na ta6e baki a zuciyata ina fad'in ka iya fad'ar R kafin kamin mazurai. Baima san ina yiba, yaje wajen wardrobe d'insa ya d'auki kayan barci yanufi bathroom. Murmushi kawai nayi, danni rayuwar mutuminnan mamaki take bani, ina dad'i kabi ka k'untata kanka irin haka? baka hira da kowa, baka dariya, shifa ko kallo inba labaraiba ban ta6a ganin yanayiba, hakama wak'a banta6a jin yana jiba, koranar dana duba wayarsa karatun Qur'an kawai nagani da Tafseer. nakai dubana gawata 'Yar kanta dakecan gefe a bedroom d'in nasa, mafi yawanci littatafan addini ne awajen, sai English Novels. (To yayi karatun addinine? tunda naji Momma tace anan India ya girma🤔). Wata zuciya tacemin su India basuda musulmai ne?. “hakane kumafa” nafad'a a fili ina mik'ewa. Ganinaima bara nacire kayana kafin yafito, daya fito saina shiga nima. Har ga ALLAH banyi tunanin fitowarsa ba yanzun, dan haka hankalina kwance na zuge zip d'in rigar, na cireta gaba d'aya, shima sket d'in nayi k'asa dashi yafad'i k'asa. Juyowarnan da zanyi da nufin d'aukar towel dana ajiye saman akwatina sai kawai naga mutum tsaye a k'ofar bathroom, hannunsa rik'eda k'aramin towel yayi tsaye yana kallona. Bansan Na kwalla k'araba wlhy, Na rarumi towel d'in nayi saurin kare jikina, ALLAH ma yaso k'ofar a rufe take, dan dawuya su Aunty Mimi sujini. K'arata tadawo dashi daga sumar tsayen dayayi, yawani kauda kansa cikeda basarwa yana ta6e baki, saikuma yaja guntun tsaki yaje bakin gadon ya zauna yana cigaba da goge fuskarsa, dan har yayi shirin barcinsa a ciki. Jinayi tamkar na makesa, d'an rainin hankali yagama kalleni zai wani miskile fuska asfa baiga abin kalloba. hijjabin sallata na janyo Na saka, sannan nawuce bayi ina hararsa. Ina shiga yamik'e yana wani munafukin murmushi, abin salla ya shinfid'a ya kabbara shafa'i da wutiri. Nadad'e abayin nak'i fitowa, saida nabar jin motsinsa duka sannan Na fito, dayake nayi shirina a bayin nima, nazata ya kwanta, amma saina iskeshi zaune a kujerar dake gefen kantar littatafan nan ya bud'e laptop yana danne-danne, gefensa kofine yanata turiri, da alama coffee ne aciki. Yad'an juyamin baya kad'an, dan haka cikin sand'a Na rufe k'ofar, nakuma tako a hankali har zuwa wajen sofa Na kwanta, duk zatona baya ganina, Ashe yana kallon duk abinda nakeyi ta gefen idonsa. A ransa yace munafunci. cigaba yay da aikinsa hankaki kwance, bai bar wajenba har kusan 1:30pm, maimakon ya kwanta sainaga yashiga bayi ya d'auro alwala. Nima har time d'in barci yakasa d'aukata, maganar Momma tanata min yawo a zuciyata, tunanin ta inda zan taimaki Galadima kawai nakeyi. Ina kallonsa ya kabbara salla. saida yay kusan raka'a 6 yanayi yana sallamewa, daganan ya d'auki alku'ani yafara karatu k'asa-k'asa. Masha ALLAH nafad'a a raina, danjin yanda muryarsa ke fita cikin karatun littafi mai tsarki, gashi yana fidda kowane harafi cikin tsantseni da kwarewa. Tun ina saurarensa har wani barci mai dad'i ya saceni, bansan lokacin daya kammala ba yazo ya kwanta. Muduka makara mukayi sallar asuba yau, dan haka shima yau a gida yayi. Bayan ya idar waya ya d'auka naga yayi kira. Bayan an d'aga daga can sukayi gaisuwa, jin ya tambayi ya Nigeria Na gane da 'yan can yake wayar. yacigaba da fad'in. “Nuren naga ka turomin hotonsa, shin a inane yake haka?”. Bansan mi akace masaba daga can, naga dai yayi kwafa, sai yace “ya maganar Minister? dan nagansa wajen d'urin aurena, ban kuma yi zaton zai zoba”. Canma aka kuma yin wata maganar. Zamansa yagyara, yakuma jingina da bangon, dayake yana kan abin salla har yanzun. “kayi k'ok'ari Nuren, yanzu abinda nakeso dakai shine, akwai yarinyarsa d'inan datake karatu a nan jami'ar Abuja, inason a sacemin ita k'arshen watannan, yanzu ka saka ana bibiyarmin komai nata, Shikuma Alhaji Balala driver n sa zaku d'aukemin, dan bincikena ya ganomin shekarunsa 30 dawani Abu yana masa aiki, kuma randa su Alhaji balala sukayi zama da Abie shine ya kaisa masarautar mu, inada tabbacin zai San wani Abu koda kad'anne, kuyi aikinku da kulawa Nuren, banason asami matsala kamar wancan time d'in, gobe kashiga birnin gayu plaza kuyi zama Na musamman da Saleem akan maganar CCTV camera data daina aiki randa abinnan ya faru, ni naso Na zauna dashi, amma kaga Momma tamatsa akan dawowata”. bayan nacan yagama magana. Yace “ok babu damuwa, zan turo maka number yarinyar, saiku bibiyeta tanan. sai anjima, ka gaidamin Mom d'ina”. Koda ya ajiye wayar saiya koma gado ya kwanta abinsa, nikam ina zaune sai cud'awa da kwancewa nakeyi, ban fahimci wayar tasaba gaba d'aya, shin wanene kuma NUREN!? shikuma miye alak'arsa da Galadima kuma?. Tabbas aikina bazai yuwuba saina San wanene NUREN, wane kuma aiki yakema Galadima a sirrence, su waye wad'annan mutanen biyu daya ambata Minister da Alhaji balala? suna cikin wancan case d'in Na Abie ne? kokuwa tasu dabance?. Kwanciya ta na juya yanda zanji dad'in tunanin da k'yau, saikuma naga ai ba sanin waye Nuren bane matsalata yanzu, kamata yayi nafara sanin shi kansa Galadima d'in da rayuwarsa, na tuna maganar Momma da tece “shi mutumne dabashi da yadda”. Mutum mara yarda kuwa yanada wuyar sha'ani, kad'an na juyo na kallesa, idonsa a rufe yake, amma ban yarda barci yakeba, na janye idona nima na maida lumshe, barcine mai nauyi ya kwasheni, harya fita bamma saniba inata barci, babu kuma Wanda yazo ya tadani. Sai around 11:30 na tashi, wani masifar ciwo kaina yakemin, haka dai na tak'ark'ara nayi wanka, nagyara d'akin sannan na sako k'asa, gidan shiru tamkar babu kowa, sai television daketa aiki, zama nayi bisa kujera dafe da kaina. “ranki ya dad'e lafiya dai?”. Bud'e idona nayi a hankali, sai naga jakadiya ce, namata murmushi tareda yunk'urin tashi zaune, “wlhy kaina ke ciwo jakadiya, halanma ke kad'aice ma a gidan?”. “subahanalla, sannu ranki ya dad'e, bara na samo miki abinci saikisha magani, eh ni kad'aice ranki ya dad'e su Sauban sun tafi makaranta. Gimbiya Mimi kuma tana asibiti itama, taga kina barcine shiyyasa tahana a tadaki”. Nace “ALLAH sarki”. Wucewa tayi zuwa kitchen, babu dad'ewa saigata tadawo da tire, a gabana ta ajiye tana fad'in “gashi ranki ya dad'e, kici saikisha magani kafin Magajin gari yadawo saikuje asibiti”. Kallonta nayi da mamaki, “jakadiya waye magajin gari kuma?”. Tayi 'Yar dariya, “ranki ya dad'e ina nufin mai gidanki, ai magajin gari nake cemasa”. Murmushi nayi ina girgiza kai kawai, na had'a tea nasha, sannan nasha maganin, anan falon na kuma kwantawa, barci yakuma kwasheni. Jakadiya na zaune tana gadina. Da sallama ya shigo, jakadiya ta amsa tareda mik'ewa da sauri ta kar6i kayan hannunsa tana masa sannu da zuwa, yad'an saki fuska yana amsawa. d'aya acikin kujerun ya zauna, sai lokacin idonsa ya sauka kaina..... maganar da jakadiya take masa ce yasakashi janye ido daga kaina ya maida kanta. “ranka ya dad'e akai kayan samane?”. “no jakadiya kibari zan hau dasu, ai sunmiki nauyi, ita wannan mike damunta tayi barci anan?”. ‘yay maganar yana maido idonsa kaina’. “kanta ke ciwo ranka ya dad'e, amma tasha magani ma, shine barcin ya kwashe a wajen”. Ido yad'an tsuramin, kafin ya cije lips d'insa kad'an. Jakadiya tajuya zuwa kitchen, babu dad'ewa tadawo da ruwa ta ajiye masa. Sannu yamata sannan yad'auka yana sha, itakuma tabar wajen. Kofin da yasha ruwan ya ajiye, ya maida kansa jikin kujerar ya jingina kansa, tareda maida k'afarsa d'aya kan d'aya, lumshe idonsa yayi, ta k'asan ido yake kallona, tsawon lokaci yana a haka, yayinda nikuma nake barci bansan yana yibama. Kamar an tasheni saina bud'e idona a hankali, dashi na fara tozali, dan haka namik'e zaune da sauri, tareda warware d'an kwalina na yafa, dan gown d'in material ce a jikina, gashi irin mai santsinan, kuma rigar takamani sosai, a raina nace dukma yagama kalleni, wama yasan tun yaushe yake anan?. Duk abinda nakeyi yana kallona, sometimes yarinyar nan takan bashi dariya, a d'an zaman dayayi da ita yalura tanada kunya, saidai batason raini, bakuma tada tsoro ko kad'an, ganin ina Neman mik'ewa saiya bud'e idonsa. Harna fara tafiya saina juyo, danjin kamar ana kallona. idonsa a kaina, amma saiya wani basar tareda janyewa. Kaina kawai na girgiza, harzan cigaba da tafiya saina tuna nemanfa kusanci nake dashi domin cika alk'awarin Momma da zanyi, baya na dawo nakoma na zauna, muryata a sanyaye nace, “sannu da dawowa”. Sosai na bashi mamaki, dan haka ya kalleni da k'yau, kamar zaiyi magana saikuma ya fasa, kusan minti 1 dawasu Second's sannan yace “mike damunki kika kwanta anan?”. “kainane ke ciwo amma yama daina”. maganar dayayice tabani mamaki. Mik'ewa yayi yana fad'in “ba gulma tasaki k'inyin barci jiyaba, dole ai kitashi da ciwon kai”. Galala nabishi da kallo, kai wannan guy d'in yafara bani tsoro, dama yasan banyi barciba jiya kenan? Anya guy d'innan baya gani har hanji🤨? nabishi da kallo yayinda yake taka step d'in benen cikeda izza, hanunsa d'aukeda ledojin daya kwashe a falon, saida ya 6acema ganina sannan na sauke ajiyar zuciya. ★*★*★*★*★*★*★ *_Nigeria_* Tun bayan zuwanmu sallama da tafiyarmu 'yan gidanmu sai suka dainama innarmu magana, musamman yanda sukaga anata fita da abubuwan dana bari a baiwa mutane, innarmu ko'a kwalar rigarta itakam, bata damu da rashin mata maganar dasukeba, harkokin gabanta kawai takeyi hankali kwance. Innaro kam kud'in da Galadima yabata suka sakata d'agama innarmu k'afa, ko gaidata tayi cikin salama take amsa mata, a jiya harda siyoma su Aryaan sllifas, wai taganine a hanya sun mata k'yau ta siya musu, murmushi kawai innarmu tayi damata godiya ta kar6a. Wannan k'yauta tasaka mamansu yaa Hameed kasa hak'uri taita sakin habaici, daga nan sauran matan gidanmu suka d'auka suma, innarmu saita saka karatun alkur'ani ma a waya tashige d'aki tarufe kanta. Har sukaci suka tsire dan kansu sukayi shiru. Kusan k'arfe hud'u na gamma saiga Zarah wujiga-wujiga tashigo gidan, ga ciki yafito masha ALLAH, Innarmu dake tsakar gida tana wankin kwanuka tayi saurin cewa “zarah lafiya?”. Jikin innamu tafad'a ta fashe da kuka, “innarsu 2 ki taimakeni zai kasheni, wlhy bani na d'auka masa kud'iba, narantse da ALLAH........” Tuni 'yan gidanmu duk sun fito, danjin kururuwar Zarah, mamansu yaa hameed tazo ta janyeta daga jikin innarmu, “k mahaukaciyar inace dabazaki nutsu kisan wazaki fad'ama matsalarki bane?”.. Oho ita Zarah ba wannan bane matsalarta a yanzun, takuma fad'awa jikin mamansun tana kuka da rantsuwar ba ita ta d'auki kud'iba. Ganin tana neman yage musu zani a kasuwa sai mamansu tajata suka shige d'aki. Wata dariyar gatsatsa maman Safara'u tayi, tareda ta6e baki tana kallon Gwaggon Haleematu dake k'usa da ita “to anfara da bismillah kenan? Wata 6 an koro yarinya da duka?...... Caraf Momy Hadiza ta k'ar6e “yo mai kashi a gindi ai baya toshe hanci yace makwafcinsa na wari, kidai iya bakinki tunda kema kinkai gidan wani”. “can a bakinki, nakai kuwa, kuma tawa zama daram babu yaji balle nik'a gari, tunda ba auren hange-hange da tauye hak'in wasu namata ba, ai bama saikin zak'eba, munsan mai kaza a aljihu dama baya jimirin Asss!, indai nice kinga tafiyata, kiyi da wani ba niba”. Tamkar Momy Hadiza zata daki maman Safara'u haka ta hayayyak'o mata, wannan hayaniya ce tafara jawo kunnen makwafta gidanmu, saiga innaro tamkar an jehota, ta shiga tambayar ba'asin hayaniyar, dansu Abbanmu duk suna wajen aiki. Duk shiru sukai mata, sai innarmu Ce da maman Fauziyya suke fad'a mata abinda yafaru. d'akin mamansu yaa hameed tashige domin jiyo ba'asin dawowar Zarah n. Itadai innarmu jikinta duk yayi sanyi, wannan zamanin ko aurar da yaranka mata kayi tsugunne bata k'are makaba, dan sai ALLAH yabasu mazaje na garin dazasu iya hak'urin zama da juna, aurene tunkan ayisa zakaga angama kwashe masa albarka wajen buruka da bidi'oin biki, ga iyaye yanzu gaba d'aya hankalinsu Yakoma ga d'irkama 'ya'yansu kayan mata kawai ba koya musu dabarun zaman aurenba, sun manta kayan mata basu kad'ai bane ma'aurata ke buk'ata a zaman aure, sudai sukan kawo wata nutsuwane da kuma dank'o cikin rayuwar auren, gaba d'aya yanzu zakiga gidajen auren Malam bahaushe sun canja, wuyarta dai akai yarinya miji ya kauda mata budurcine, wata biyu yayi yawa kwarnafinsa ya kwanta saiya fara Neman makusarta, gakuma yaran basuda wata dabara dazatasa su taka tsantsan ga zamantakewar, har yakai an sami sassaucin cin zarafi daga mazajen nasu, to an nuna musu kayan mata sune kawai jigon aure da hangar mallakar mijin kansa, to ALLAH ka zaunar mana dasu lafiya dai agidajensu. Nace amin innarmu😘👌🏻 ★★★★ Kusan minti 10 da shigarsa saina tashi nabi bayansa, waya nakeson ya aramin nayi kiran su innarmu Susan mun sauka lafiya. Saida nai sallama yabani izinin shiga sannan, saman sofa na iskeshi zaune yana latsa waya, da alama waya yagama ko zaiyi. Zama nayi a kujerar da yake karatu takusa da kanta, na kwantar da murya cikin sigar ladab nace “yalla6ai ka aramin waya dan ALLAH nayi kiran innarmu da Munubiya”. Biris yay dani, sai zuwa can yad'ago ido ya kalleni, ya motsa baki zaiyi magana amma jin kai ya hanashi, saiyay shiru kuma yacigaba da latsa wayar, saida yamula dan kansa sannan yajawo ledar daya shigo da ita, wata k'aramar pink d'in souvenirs bag yamik'o min batareda yace uffanba. Tasowa nayi zuwa gabansa zan kar6a, hanun bag d'in k'aramine, dan haka hanunmu ya had'u waje d'aya, ni da shi kowa saida yaji shock, yay saurin janye hannunsa, yayinda bag d'in tayi k'asa zata fad'i yay saurin kuma k'ok'arin tarewa kamar yanda nima nakawo hannun hagguna da sauri. Sai kawai na damk'e hannunsa kanmu ya gwaru waje d'aya. Kowanne dafe kansa yayi da sauri, yayinda hanun damarsa dana hagguna suke tallafe da juna mun tare bag d'in karta fad'i. Na kallesa tamkar zanyi kuka, dan wlhy naji zafi, kansa kamar kwakwa☹. Hararata yayi yana fad'in “k wane irin kaine dake haka?”. Haushi saiya kamani, shi baiga nasaba sai nawa, na matso kwallar dasuka cikamin idona, cikin turo baki nace “kana niyyar fasan kai, shine zaka maida abun kaina?”. Hanunsa daya dafe kai yasaka ya d'an bugi bakina, “k kinma rainani wlhy”. K'asa na durk'ushe kawai nasaki masa kuka. ya waro ido da mamaki yana kallona, wannan d'an abin dayamin shine na kuka? yarinyar nan akwai rainin hankali fa”. Ganin abin nawa azimunne saiya mik'e tsaye, tareda d'iremin wayarsa bisa cinyata ya shige bathroom. Yana shiga nama bayansa gwalo, dama duk cikin takune, sonake kawai nagano lagwansa. goshina nad'an shafa dan gaskiya naji zafi, saima naji wajen kamar yafara kumbura. Ban tashi a wajen ba nashiga loda numbar innarmu, amma tak'i shiga, saina saka ta Munubiya, itama tak'i tafiya, nad'an ja tsuka, ina kuma shafa goshin, kamar wasa wajen sai rad'ad'i yakemin, ina cikin mulmulawa da matse baki yafito, kallona yad'anyi kamar zai basar saikuma ya kasa, ya k'arasa jikin wardrobe d'insa yana bud'ewa, “har yanzu goshin zafi yake?”. Kamar zanyi kuka nace, “eh wlhy ”. Daina abinda yakeyi yayi yajuyo yana kallona, saikuma ya maida drowan yarufe yanufe inda nake zaune. A gabana ya d'urk'usa, k'amshin sabulun wankan ya daki hancina, hannunsa na haggu ya d'aura bisa kaina, ya d'aura na damar akan goshina, sanyin damshin ruwan da taushin hannunsa suka ratsa goshina, a hankali yafara mulmula goshin, nafara matse baki ina rik'e hannunsa, dan wlhy akwai zafi, “please kabarsa dan ALLAH, wlhy akwai zafi fa”, bai saurareniba, duk rik'e masa hannun danake saida ya mulmulamin sosai sannan yamik'e yana hararata da ta6e baki, “halan kekam kina jaririya ba'a miki wankan jegoba?”. Baki na tunzuro masa, nace “ka kira innarmu ka tambayeta mana, ni ina zan sani”. Batareda ya shiryaba ya murmusa yana barin wajen. Kayansa ya d'auka yakoma bayi danya sanya. Nikuma saina mik'e nakoma kan sofa d'in ina bud'e bag d'in d'azun. kwalin wayane mai k'yau, wani dad'i ya kamani, amma saboda jan aji saina maida na ajiye gefena, nacigaba da danna kiran su innarmu. A haka yafito ya sameni, yana sanye cikin Brown d'in wando da Navy blue t-shirts mai gajeren hannu, ya tsuke k'ugunsa, bai kalleniba yawuce wajen wani kwando mai k'yau da aka zuba sandunan wasan Golf a ciki🏑, guda biyu ya ciro, sannan ya tako inda nake yana fad'in “bani wayata idan kin gama”. Fuska na marairaice nace “ALLAH kagani bamma yiba, tak'i shigama”. Wayar ya kar6a ya duma number, bakinsa ya d'an ta6e “k bak'auyar inace dazaki kira number a haka? ko nan k'asarkice?”. Tunawa nai da saina saka + ashe, nace “oh namanta saina saka + wlhy”. Aljihu ya saka wayar, “saiki bari sai wani time d'in kuma, yanzu sauri nake ana jirana”. Da sauri nace “zan bika please, wlhy gidan shiru babu dad'i”. Yana fesa turare yace, “ba yauba, baga jakadiya nan a gidanba, yanzu kuma Khumar zai d'akko khaleel a school ai”. Shiru nayi bance komaiba, saiya juyo ya kalleni, ganin na kwa6e fuska cikin damuwa saikuma yaji wani iri, juyawa yayi yagara kwalar rigarsa, kafin yaje drowan gefen gadonsa ya d'akko wasu album na pictures har hud'u, saman cinyata ya ajiye batareda yace uffanba, yakwashi sandunansa yakama hanyar fita, batareda ya juyoba yace “wad'annan kayan nakine ki duba”. Kafin nabasa amsa harya fice abinsa. Kaina na girgiza ina ta6e baki, a fili nace, “Alaramma mara R ALLAH ya gyarakama Momma kai dai”. (Kifad'a a gabansa mana yarinya. 🤣🤭). _______________,,___________,,,______ Da sauri mamansu yaa Hameed ta kwa6e bakin Zarah alamar tayi shiru, saboda shigowar innaro, innaro bata kulaba, dan haka ta zauna a kujerar falon idonta akan Zarah, ganin yanda duk jikinta shatin duka, “kekauwa zara'u miya sameki haka? Ga ciki?”. Harara mamansu yaa hameed taketa zubama Zarah, amma ina bata kulaba, ta share kwallar fuskarta tana fad'in “innaro wai kud'i ya ajiye a gidan jiya, shinefa yaduba yau bai ganiba, ina kitchen yashigo yana tambayata wai kona canja musu wajene? shine nace bammasan yashigo da kud'i gidan ba bare harna canja musu waje, ko rufe baki bai bari nayiba ya fallamin mari, nikuma naji zafi namasa ALLAH ya Isa, shinefa kawai yacire belt d'in jikinsa yahau buguna, wlhy da k'yar nagudo na fito, nasan idan nashiga gidan Siyama zai iya bina har can, tunda gidan d'an uwansane, dak'yar nasamu napep a anguwar nataho gida”. Innaro tarik'e ha6a tana fad'in “oh ni marwanatu jikar Falalu, yanzu shi Sa'eedunne yamiki haka da hankalinsa? toke kin tabbata baki d'aukar masa kud'iba?”. “wlhy innaro ban d'auka ba, kinji na rantse miki, shi dama halinsane haka?, indai ransa ya6aci ko kika masa kuskure sai dai kawai kiji mari, wlhy zuwana gidannan tun bankai satiba yake marina idan namasa Abu, yaune harda duka, gashi ko kad'an bashida hak'uri, Abu kad'an yagani saiyayi tsogumi, idan kuma kin masa na kirki bazai yaba mikiba, dawuya kimabasa Abu sau 10 bai kushe 8 a cikiba, 2 kuma bawai zai nuna yaji dad'i baneba😢”. “kai amma wannan yaro anyi wulak'antaccen yaro, yoshi dama dukan mata yake akasa nabashi jikata? Bari su Auwalun suzo, koti zansa su kaishi, sai an kwatar miki hak'inki,”. “nidai babu wani court k innaro, kawai akirasa amasa bayani a sasantamu nakoma d'akina, inason mijina wlhy”. “enyeee! A lallai zara'u kinkai kuwa, nikike fad'ama kina son mijinki? to dan ubanki auwalu saiku tashi ki koma yanzu, idan yagadama anjima akiramu jana'izar gawarki”. fuuu tafito tana sababi, kayaya tunta da maimaita maganar da Zarah tafad'a mata yasaka 'yan gidanmu fahimta komai, wasu dad'i har tsakar kansu, (yo dama gidanmu kowa bawani son d'an uwansa yakeba, salon munafurcine kawai da bariki na tsoffin mata). 'Daki Momy Hadiza tashige takira Siyama danjin k'arin bayani, anan Siyaman ke sanar mata wai dama ba wannan ne karon farko da Sa'eed d'in yay Complain Zarah na d'auka masa kud'i ba”. Momy Hadiza ta rabga salati tana fad'in “k 'yarnan da gaske?”. “wlhy kuwa Momy, yanzu haka ma gashi anan gidanmu suna maganar da Sulaiman”. “to ALLAH ya k'yauta, ni dama auren ya mutu ki zauna daga ke saike, danni bama na k'aunar wannan had'in gambizar family d'in, komai yaro yamaka ido nakai”. “yo nifa Momy wlhy yanzu haka bama magana da Zarah, daga ranar mun had'u da ita a gidan sunan Hanan k'anwarsu, toni shine ya kaini da kansa, itakuma Ashe bashi yakawitaba, shine ta tambayeni miyasa ban biya mata mun taho tareba? Nace mata ai shine yakawoni, itama nazata Sa'eed d'inne zai kawota, shinefa taketa faman fushi da gaba dani”. “eye, kice tafara miki hassada kawai saboda taga mijinki tafi kulawa dake? to wlhy bance ki d'aga mata k'afaba, karma kituna da ubanki da ubanta ciki d'aya suka fito”. “insha ALLAHU Momy bazan raga mataba”. “yauwa 'yar albarka. Yanzu yamaganar kud'in damukayi ranar? kinsan fa bikin nata tahowa?”. “zan aiko miki Momy, wai Momy da gaske Munaya bata Nigeria? ”. Tsaki Momy Hadiza taja, cikin bak'in ciki tace “haka dai iyayenta sukace, mudai bamuda tabbas tunda ba'a gabanmu jirgin yatashiba, anzo dai mana sallamar munafunci itada wannan miskilallen mijin nata”. “aikam Momy indai da sunzo d'in to da gaskefa sun tafin, dan Sulaiman yacemin yaga Galadima a airport shekaranjiya da sister d'inan watawa, shikuma yaje raka babansune zaiyi tafiya”. “suyita tafiyar mana, kema dan sakaraice ai, yo mi mijin nata yafi naki? Amma kod'an Honeymoon d'in nan da ake zuwa ke kin kasa sakashi ya kaiki”. “lallai momyn nan, shikenan tunda laifina kike gani, nidai zan kiraki anjima, yanzu jirana suke nakai musu abinci”. ‘bata jira cewarta ba ta yanke wayar’. Takaici yakuma kama Momy Hadiza, saitaja tsaki, amma saboda munafurci saita nufi d'akin mamansu yaa Hameed jiyo abinda ya maido Zarah gida. (Fuska biyu😆👿). ******************* Hotunan na ajiye nafara bud'e wayar, woow irinfa wayarsa ce komai da komai, saidai tawa pink ce, gakuma extra condom na wayar har kala uku, kai gsky wayar tayi babu k'arya, layin dana gani a ciki na d'auka na saka sannan na jona charge saboda d'oki, sauran ledojin nahau bud'ewa, duk kayan sawane k'ananu marasa nauyi, kuma bamasu fidda tairaiciba, zan iya sakasu gaban kowa, a raina nace Ashe Galadima yanada kirki haka?, saida nagama had'a kayan waje d'aya sannan na haye gadonsa da yaune karon farko zan haushi, nawani 6ararraje ina kallon hotunan, wasu hotunan abin dariya wlhy, dan wasu yana yarone k'arami, wani a makaranta, wani awajen wasan yara, wani a masarautarsu, wani tareda mom, wani da aunty mimi da sauban, duk inda suke da Abie saida nayi kuka, dan abie duk yana kwancene, k'alilanne yakeda lafiya sannan. wasu kam ya zube wayoyi yanata had'e-had'en abubuwa na wasan yara😄. Kallon hotunan ne suka d'aukemin hankali har wani lokaci dasu Sauban suka dawo, bamma san sun dawoba saida Samha tahawo saman. Zama tayi tanamin bayanin wasu mutanen jikin hotunan muna dariya, bamu sakkoba saida Sauban ya hawo yakiramu. ****** Sai bayan isha'i suka dawo shida aunty mimi. Ina d'aki zaune har sannan ina kallon pictures d'in ya shigo, d'ago kaina nayi na kalleshi tareda amsa masa sallamar. Namasa sannu da zuwa. Ciki-ciki ya amsa yana zubewa bakin gadon, d'an kwanciya yayi kusan minti 10 kafin yamik'e yashiga bathroom, kusan 1hour sannan yafito maybe su yalla6ai an sauke nauyine (🚽🤭). Yau saida na jirasa harya idar da shafa'i da wutirinsa, dan magana nakeson muyi, ganin ya idar ya zauna latsa wayane nace “dan ALLAH yalla6ai in tambayeka?”. Batareda ya d'agoba yace “uhmm”. Zamana na gyara cikin nutsuwa nace, “shin tunda Abie yafara jiyya anta6a masa maganin gargajiya ko amaida hankali ga addu'oi haka?”. Yanzun kam d'ago ido yayi ya kalleni, dama tunda nafara maganar ya dakata daga latsa wayar. “lips d'insa yad'an cije, kamar zaiyi magana saikuma yay shiru. Nace “kayi hak'uri idan nashiga hurumin daba nawaba”. Nanma shiru yamin, saida yaja wasu mintuna kafin ya ajiye wayar yagyara zamansa, cikin alamun bak'in ciki yace, “duk an gwada masa, saidai gaskiya bakamar yanda aka maida hankali gana asibitinba, saboda anriga da an sanar mana Allurar gubace aka masa, amma muna k'ok'arin sakashi a sallalolinmu na farilla dana nafila. Kullum addu'oinmu akansa yake”. Ajiyar zuciya na sauke, nace “ALLAH yabashi lafiya, yakawo mana iyaka, yakuma bashi ikon cinye jarabawar nan”. “amin yafad'a a la66ansa”. Dagani harshi babu Wanda yasake magana har muka kwanta, saidai yauma banyi isashen barciba, inata cud'awa da kwancewa, har gabannin asubahi kafin barcin ya saceni..................✍🏼 _To Alhmddlh my sweet fans, zamu dakata anan kenan, saikuma ALLAH yakaimu bayan salla darai da lafiya, zanbar wannan a matsayin *RAINA KAMA..... PART ONE* yanda zamu tafi a tsare kawai, basai mundawo ba kuma mushiga tunanin inama aka tsaya? Ina kuma za'a tashi, a *RAINA KAMA PART TWO* zamuga yanda Munaya zata taimaki Galadima kamar yanda Momma ta buk'ata, shin zai bata had'in kaima Kuwa? domin kunji Momma dai tace bashida yarda? ya matsayin auren Zarah? Muftahu yaya zata kasance idan Galadima ya cafkoshi? shin Munaya tanada wani fikra ne game da ciwon Abie?. wannan amsoshin duk suna cikin *RAINA KAMA PART TWO* da zaizo bayan sallah insha ALLAHU my guys, one Luv😍😍😍😘😘😘🥰👌🏻_ _tabbas banida bakin godiya a gareku, saboda addu'oi da mahaifina ke samu agareku, Comments naku suna matuk'ar sakani a farinciki sosai, ngd ALLAH yabar zuminci, duk inda masoyin wannan buk yake yasaka aransa yana can k'ark'ashin zuciyar Bilyn Abdull.🥰🥰🥰🥰😍😍😍😍😘😘😘😘😘😘😘👌🏻🤝🏻._ _ga azumi zamu shiga, 'yan uwana dan ALLAH mu maida hankalinmu ga ibada, sadaka da k'autatama marasa k'arfi, marayu,, k'autata mu'amullarmu da jama'a dayin amfani da abinda malamai zasu fad'akar damu, karya zam kullum muna wahalar zuwa tafseer amma bamu d'aukar komai, da bayan salla yawuce munkuma koma kan munanan ayukanmu, karmu manta irin wannan watan saikuma mai rabon gani, sau 1 tak yake zuwa mana akowacce shekara, wani yawuce agaresa kenan har Abadan, zata iya yuwuwa nice ma😭, zata iya yuwa kece 'Yar uwa👉🏻😭, zata iya yuwa kaine d'an uwa👉🏻😭. dan ALLAH mu gyara please & please, muyi amfani da damarmu kafin ta kufce mana, (kullu nafsin za'ikatul maut, kowane rai saiya d'and'ani mutuwa, ubangiji bai turo maka date d'in da rundunar mala'iku zasuzo d'aukar rayin nakaba,😭 mutuwa bata kwankwasa k'ofa, batada wata alamar yanda zatazo ta riskeka, kana tafiya ne, ko kana barci, ko kana salla, ko zaune, ko kana hira, ko kana aikata wani sa6o, ko kana wani abin alkairi😭, ya ALLAH ka d'auki ruhinmu muna masu imani agareka da tsoranka, ALLAH ka gafarta mana, kamana maganin abinda muka Sani da wandama bamu saniba._ _ina rok'on dukkan Wanda na 6atamawa a yayin wannan rubutun ko kafin shima dan ALLAH Ya gafarceni, nidai na yafema kowa._😢👏🏻 *_duk masoyina na gaskiya Dan ALLAH inason yasakani a ddu'arsa ta cikin azuminnan koda sau d'ayane, idan munada Rabon haihuwa adunaya nida mijina ALLAH ka azurtamu da samu masu albarka cikin sauk'i da rahamar ubangijin talikai, idan ba alkairi bace agaremu ALLAH kasamana hak'uri da juriyar azuciyata😭👏🏻, ALLAH kayaye mana dukkan damuwarmu baki d'aya._*😭👏🏻 Dan ALLAH ko sau 1 yane kar'a manta dani🙏🏻😊 Amin afuwa zan rage groups saboda yawan groups d'in suna cimin data wlhy, idan nayi sub na wata d'aya ko sati bata yimin take k'arewa🙏🏻. Ngd sosai, ALLAH yabar zuminci, ALLAH yasa munada rabon sake had'uwa a bayan salla, ALLAH ka kar6i ibadunmu baki d'aya. yabamu juriya da hak'urin ibadar dake tunkaromu nanda kwana 1👌🏻. Happy Ramadan Advance😊🥰🥰🥰🥰😍😍😍👍🏻 Binyn Ku Ce dai👌🏻 Writer✍🏼 *Abdul-maleek bobo!!* *Auren k'addara ko biyayya!?* *Ban saketa ba!!* *Ciki da gaskiya...!!* *Karayar arzeek'i!!* *k'anwar uwace ko kishiyar uwa!?* *Kukan krciya...!!* *Ni da Aminiyata!!* *Nawaff!!* *Rashin Sani!!* *Raina kama.....!!* *Sabon Al-amaree!!* *Sanadin bikin salla!!* *Siyasa ko k'abilanci!?* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ____________________________ *_Dolene page d'in farko yazama sadaukarwa agareki MAMAN JUNIOR😭, ALLAH ya gafarta miki, ya raya abinda kika bari, ALLAH ya k'addara bazakiga k'arshen wannan littafiba. (Masoyan Raina kama kusaka wannan baiwa a addu'arku, ta rasu cikin azumi, kusanma k'arshe, member ce a group d'in raina kama, ALLAY ya yafe mata🙏🏻😭._* _INA fata kunyi salla lafiya gaba d'ayanku, ALLAH ya kar6i ibadunmu. Ya yafe mana, yasa kar6a66iyar ibada mukayi🙏🏻😭._ Sai dai banci naman salla ba sosai, gashi banida d'inkin dallah🤦🏻‍♀🤥. ______________________________ ~Book 2~ 👉🏻1⃣ .............Tunda mukayi maganar nan dashi banyi k'asa a gyuwa ba wajen dagewa da addu'oi wa mahaifinsa, ina buk'atar ruwan zam-zam, dan haka yau nashirya fad'a masa ya nemomin. tunda safe ya fice, dan haka bamuga juna ba. Yauma dai haka Na tashi banida wata isashshiyar lafiya, Na tak'ark'ara nayi gyaran d'akin har zuwa falo, sannan Na had'a ruwa mai zafi nayi wanka dashi. Ina cikin shiri najiyo sallamar Samha a k'ofar falon, rigar dana fara sakawa Na k'arasa, sannan nace ta shigo. “humm Aunty gimbiya kina kallon kanki a mirror kuwa?”. Cikeda mamaki Na kalleta sannan Na kalli jikina, nace, “kamarya?”. Zama tayi a sofa tana 'yar dariya, sannan tace, “wlhy kinyi k'iba, sati uku kacal da zuwanmu India kin koma wata madam”. Nad'an fiddo idanu waje, sannan Na harareta, “lallai Samha nagode da zagi to”. “tab wlhy babu wani zagi gaskiya Na fad'a, halan Uncle Sam bai ta6a fad'a mi ki ba........” Ta k'arasa Maganarta da d'ai-d'ai saboda shigowarasa d'akin da sallama ciki-ciki. Suna had'a idanu ya watsa mata harara, hakan ya tabbatar mana da yaji maganar tata, da sauri tamik'e ta fita, Nikuma najawo gyalena na yafa sannan Na kallesa. Saman sofar ya zauna ya dafe kai, kallo d'aya zaka masa ka karanci damuwar dake shimfid'e bisa fuskarsa. “yalla6ai lafiya kuwa?”. ‘nafad'a cikin tausayawa’. Shiru bai amsaniba, banyi zuciyaba nataka a hankali zuwa gabansa, durk'usawa nayi a gaban nasa, a d'arare nasa hannu Na najanye nasa dayay tagumi dashi. Ya d'ago idanunsa da sukai jaa yana kallona. kasa jurar kallon cikin idonsa nayi, Na janye nawa gefe, cikin dakiyar zuciya nakuma fad'in “bakada lafiya yalla6ai?”. Yanda nayi maganar a marairaice saiyaji yakamata ya fad'amin, kodan nuna damuwar danayi akansa...... Ganin yamin shiru nikuma saina yink'ura natashi ina fad'in “kayi hak'uri idan nashiga hurumin daba nawab......” Bankai k'arshen maganarba naji tattausan tafin hannunsa cikin nawa. Rintse idanuna nayi, saboda wani yarrr da tsigar jikina tayi, shima agaresa saiya lumshe idanu kawai. najuyo danufin zare hannun kawai ya fisgoni na fad'a saman kujerar, rabin jikinna duk yana a jikinsa, yayinda sauran rabin nake a kan kujera. Bansan nawani lumshe idanuba saboda daddad'an k'amshin turarensa d'aya ratsa hancina zuwa magudanar jinina. shikuma ya sauk'e 6oyayyiyar ajiyar zuciya. Ya karkato da fuskarsa inda tawa take a gefen kafad'arsa har inajin saukar numfashinsa saman face d'ina, mayun idanun nan nasa suka kuma shiga cikin nawa, na janye da sauri, sannan nafara k'ok'arin cire kannawa daga kafad'arsa. Hannunsa na dama da nake jiki ya sak'alo ta bayana, ya maida kai na ya kwantar a kafad'ar tasa, cikin muryarnan tasa mai kama da anmasa tilas yace, “jikin Abie ne ya motsa, Ashe tun jiya basuyi barciba gaba d'aya, da safennan Akash yakirani yake sanarmin, nakasa kallon halin da mahaifina yake ciki Munaaya! Abie na yana cikin mawuyacin hali..” ‘yak'are maganar cikin zirarowar kwallar data cika masa idanu tunda yafara maganar’. Wani matsanancin tausayinsa ne ya ratsani, duk jarumtar Galadima kaga yana kuka ai kasan lamari ya 6aci gaskiya, nima hawayen suka fara gudun fanfalak'e a kumatuna, tashi nayi zaune sosai, cikin wata jarumtar da bansan inada itaba nasaka hannu Na kamo hannunsa cikin nawa. Sai kawai naga ya zame sosai ya kwantar da Kansa bisa cinyata, tareda hard'e hannayensa a k'irji. duk da kujerar tama tsawonsa kad'an, dan ma Love's chair ce. Kansa nafara shafawa a hankali, hawaye na zirara daga idona har yanzun. Shikam idanunsa a lumshe suke. Cikin tausasa harshe da tsantsar Nuna kulawa da tausayawa nace, “Yalla6ai kayi hak'uri, Abie d'inmu yana buk'ar addu'armu ne fiye da kukanmu, sannan itace jarabawarsa, wad'anda suka aikata masa hakan summa kansune, domin ALLAH bazai barsuba. idan ka amince akwai wasu addu'oi Dana Sani, Nina kakanmu ne yabama innarmu kafin yarasu, shine ta koya mana, mizai hana ka samo mana zam-zam muma mu farayima Abie su, Ubangiji gafurun rahimunne, babu abinda ya gagaresa, kuma shine yace mu rok'esa zai amsa mana”. Tunda nafara maganar bai bud'e idonsa ba, nikuma ban fasa shafa masa kaiba. Saida nakai k'arshen zancen sannan ya bud'e lumsassun idanunsa dasuka koma launin jaa a kaina. yamotsa baki kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru. Nima shirun nayi ban sake yink'urin yin magana ba, nadai cigaba da shafa kan nasa a hankali. ba akai 3minutes ba barci ya d'aukesa, sai numfashinsa danaji yakoma sauka a hankali. Ajiyar zuciya na sauke kawai, na tsurama fuskarsa ido, yaune ranar farko dana ta6a nutsuwa namasa kallon tsaff, sosai yake kamanni da dukkan iyayensa, Abie da Momma, amma yafi tsananin kama da Momma gsky, duniyar tunani nafad'a batare dana fargaba, tausayin Galadima da families nashi yana cukurkud'ar ruhina, insha ALLAH nayi alk'awarin bada gudun mawa a duniyarsu har zuwa lokacin da aurenmu zai k'are. kaina na jingina da jikin kujera, nima sai barcin ya kwasheni, dama bajin dad'in jikina nakeyiba. ******** Bayan anma Abie allurar datake temaka masa yin barci mai nauyi idan jikinsa yamotsa irin haka su Momma suka sami nutsuwa, dan yayi barci. Sai alokacin hankalin Momma yadawo kan Neman Galadima, tabbas taga yafita hankali a tashe lokacin da Abie ke fidda numfashi a wahale, amma hankalinta bai koma kan Galadiman ba. Aunty Mimi ta kalla tace, “Mimi ina d'an uwanki?”. Itama aunty Mimi sai yanzu hankalinta yadawo ta farga babu Galadima d'in, hankalinta a tashe tace, “Momma inagafa ya fita, bara na duba”. Bata jira cewar Momma ba tafito daga d'akin da sauri. ganin babu Galadima a wajen hankalinta yak'ara tashi, fitowa tayi harabar asibitin tana tambayar securitys d'in wajen. d'aya ya sanar mata ya fita a rikice gaskiya, dan suma sun nemi su taimaka masa amma baima tanka musuba. Innalillahi tashiga ambata. Bata koma wajen Momma ba tashiga mota tanufo gidan. Ta iske Samha a falo kwance, ko sauraren sannun datake mata batayiba tace, “k ina Uncle d'inku?”. Samha tace, “yana sama Mummy”. Da sassarfa ta haye step's d'in, itadai Samha da mamaki taringa binta da kallo. Ko knocking bata tsaya musuba ta turo k'ofar ta shigo. Ajiyar zuciya ta sauke dan ganin Galadima kwance, kansa bisa cinyar Munaya, hannunta d'aya na bisa Kansa, yayinda shikuma yarik'o d'ayan hannun munaya ya had'e da nasa ya d'ora kan kirjinsa, suduka barci ya kwashesu a haka. cikin sand'a ta juya ta fita taja musu k'ofar tana share hawaye dayima ALLAH godiya d'aya bama d'an uwanta mace tagari wadda take kulawa dashi. inda dane kafin yayi aure shima sai ciwonsa yatashi saboda damuwar dazai saka Kansa akan motsawar jikin Abie, amma gashi yanzun yasamu mai kwantar masa da hankali, suma kuma nasu ya kwanta suji da Abie kawai. Momma ta kira ta fad'amawa dan hankalinta itama ya kwanta. Momma harda hawayen farinciki, tana godema ALLAH. Aunty Mimi bata zaunaba suka koma asibitin itada Samha da tace zata bita, itama sai yanzu takejin jikin Abie ya motsa. ************* A k'alla munyi barcin 47minute's, Galadima ne yafara farkawa, ya bud'e idanunsa a hankali, hannuna dake rik'e a nasa yafara kallo, kafin yad'ago ido zuwa kaina, yamin kallo kusan na 2minutes sannan yad'an motsa da nufin gyara kwanciya, saina bud'e idona, ido muka had'a, kowa yay saurin janyewa cikin basarwa, hannuna dake kansa na cire, sannan nazame Wanda yarik'e d'in, dan wata matsananciyar kunya ce kuma takamani. Shima sai ya tashi zaune sosai, a hankali yacemin “thanks”. Daba kusa dashi nakeba ma bazanjiba. Bance komaiba, shima bai sake cewa komaiba yamik'e tsaye. takalmansa kawai yacire ya d'auki jallabiya a wardrobe d'insa yashige bayi. A hankali na sauke ajiyar zuciya, tareda janye idona daga k'ofar bayin, komai banceba nakuma zamewa saman kujerar na kwanta. Ya d'auki adadin wasu mintuna masu tsawo kafin yafito sanye da jallabiya ruwan toka, da alama wanka yayi, kallona yayi batareda yayi magana ba ya nunamin agogon dake ajiye a drowan gefen gadon alamar time d'in salla yayi. Kaina kawai na girgiza na mik'e, zuciya ta na mamakin hali irinna Galadima. Shikam turare kawai ya d'auka ya fesa yafice salla. ★★★ ((★))(())((★)) ★★★ A gidanmu kam hankalin mamansu yaa hameed da Zarah a tashe yake, dan babu Sa'eed babu labarinsa, kira Zarah tamasa yafi 50 amma yak'i d'agawa, ta tura massages babu reply, bata aikin komai sai kuka, ga ciki. Abbanmu kuma jin sanadin sawowar tata gida yace bazai kira Alhaji halliru ba har sai Zarah tafad'i ainahin gaskiya, danshi bai yarda ba itace ta d'auki kud'inba.. Innarmu dai dasuke zagi suna kallonta mak'iyarsu batakai komaiba itace tashiga lalla6a Abba damasa magiya. Itama da farko buris yay da ita, saida yaga tanace sannan yace, “wai kekam Ai'sha miyasa kika damu kankine? kinbi kin damu da lamarin wad'anda basu damu dakeba, na tabbatar da Munaya ko Munubiya ke cikin wannan halin su murna zasuyi a gidannan”. Murmushi innarmu tayi, cikin kwantar da murya tace, “Alhaji ai daga Zarah harsu munubiya duk d'ayane a wajena, domin kaine mahaifin Zarah, dukkan abinda kuma yakasance naka ina kaunarsa fiye da zatonka, a duba lamarin yarinyar kodan abinda ke gabanta, ba'a son mace mai ciki da shiga tashin hankali, muyima tufk'ar hanci tun munada sauran dama, basai Abu yayi tsamariba kuma muce zamu nemo mafita, hannunka baya ru6ewa ka yanke kayar alhaji, dan ALLAH kayi hak'uri kaji”. Jawota yayi jikinsa ya rungume yanamai saka mata albarka da aminta da buk'atarta na kiran senator halluru da safe insha ALLAH. Innarmu tamasa godiya itama. ********** “Babyna wai mike faruwane haka?”. Da gyar Munubiya ta d'ago ido daga kwancen datake a kujera ta kalli yaa Marwan dake mata tambayar. Ta shagwa6e fuska tace, “wlhy Yaya jikinne babu dad'i, kamar jiya sai kwankwatsa kasusuwane keyi”. Zama yay kusada ita, yad'ago kanta ya jinginata a jikinsa yana ta6a wuyanta, “please ki yarda muje asibiti adubaki mana?”. “a'a dan ALLAH Yaya, wlhy banason zuwa, kabari muga kwana biyu idan bai dainaba saimuje d'in”. “Amma kuma k'ya zauna da ciwo, ki daure dai, kinga ko abinci kin kasa mana fa”. “babu damuwa Yaya, yanzu zan tashi na d'ora, dan zazza6inma ya sauka ALLAH”. “Ana dai so aima Yaya wayo kawai”. Murmushi tayi tana tashi daga jikinsa,, takama hannunsa ta sumbata sannan tatashi tafice daga falon. Binta kawai yay da kallo yana murmushi, yana k'aunar matarsa kuma 'Yar uwarsa, gaba d'aya Munubiya ta canjashi, dukda bawai miskilancinsa yabariba, itace kawai yanzu baya iyama miskilancin nasa, komai a d'auren da fuskarsa take da zarar ya tunkaro gida zakiga yafara sakin murmushi, balle yay tozali da fuskar tauraruwar nan tashi mai haske da kawalwalniya a zuciyarsa. Mik'ewa yayi yabi bayanta zuwa kitchen d'in danya taimaka mata da aikin, dan yau d'in weekend ne baije aikiba. dan yayi resume tun last week. ((★))*((★))*((★))*((★)) Tunda na idar da sallar nazame a wajen na kwanta, bawai barcin nakeba, jikinane kawai da baya min dad'i, jinake kamar ana kwankwatsamin kashin jiki, sallamarsa tasakani d'ago ido na kallesa, sannan na amsa ciki-ciki nima. Frigate ya bud'e ya d'auki ruwa yakoma saman sofar ya zauna, murfin kawai ya 6alle ya hau kwankwad'a, saida ya shanyeshi tas sannan ya ajiye goran yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. nikam na k'ura masa idanu nakasa janyewa. saida yad'ago muka had'a idanu sannan nayi saurin yin k'asa da nawa. Shi bai janyeba yana kallona yace, “tashi muje hospital d'in, daga nan saimu samo zam-zam d'in”. Tunkan yakai k'arshen maganarma na mik'e tsaye, hijjab kawai nasaka nad'an gyara fuskata, shikuma ya d'auki kaya yashiga bayi ya canjo sannan muka fice. Jin gidan shiru yasashi d'aukar waya yakira sashen bayin gidan, babu dad'ewa saiga d'aya acikinsu tazo. Zubewa tayi tana gaishemu, ya d'aga mata hannu yayinda nikuma na amsa. yace, “ina Samha?”. “Ranka ya dad'e sunfita suda mummy”. Yasan aunty Mimi take nufi, dan haka bai sake cewa uffan ba yafice abinsa. sai nice nace tatashi taje, sannan nabiyoshi abaya. Sai da yasakama k'ofar security sannan muka nufi wajen motarsa, bayin dake zaune a harabar gidan maza sukazo da sauri suna gaishemu, hannu kawai suma ya d'aga musu muka shiga motar, suka bud'e mana gate d'in muka fice. Tunda muka fita babu Wanda yay magana tsakanin ni da shi, yana aikin tuk'insa da sauraren redio daya kunna a motar, nikam ina lafe a kujera ciwo ya isheni, dan bana fahimtar yaren dasukeyi a redio d'in, tunda ba English baneba gaskiya. Mun Isa wani babban shagon Islamic camix, komai zaka iya samunsa daya shafi maganin muslinci. Abinda ya kaimu muka shigayi, yad'ebo zam-zam dayawa, sannan ya kalleni yana fad'in “saikuma mi?”? Shiru nayi ina nazari. Dame yakamata muk'ara?, zuwa can nad'an hau duddubawa ina karanta sunayen magungunan ajikin kwalin, duk maganin danaga zai iya shafar jinnu ko sihiri, saida na d'akkoshi, (a tunanina idan mun dawo gidan zan d'auki hotunansu na turama Munubiya ta bincikamin yanda yadace ayi amfani dasu. Duk abinda nake yana a tsaye yana kallona, saida na kammala sannan nasanar masa na gama. Mun k'arasa wajen biyan kud'i, bayan yabiya yaran shagon d'aya ya d'aukar mana zuwa mota. Daga nan asibitin muka nufa, mun tarar har lokacin Abie yana barci, sai gaisawa nukayi da momma da aunty Mimi, duk sunji dad'in yanda sukaga Galadima cikin nutsuwarsa. Zama yay kusada Abie yana mai tsurama masa idanu da masa addu'oi samun lafiya a zuciya, da kuma kudirar binne Wanda ya cutar masa da mahaifi da ransa idan ya kamashi a hannu. Momma tayi farinciki da yanayin Galadima d'in cikin k'oshin lafiyarsa, dan da a dane da yanzu shima yana gadon asibitin, amma Alhmdllh yanzu gashi normal. Mukam ni da Samha muna gefe zaune muma, ba hira mukeba, kowa yayi shirune yana tunanin duniya. Sauban ma yana dawowa daga school shida Khaleel nan suka taho. Bamu bar asibitinba sai dare, harda Momma muka wuce, dan yau suna buk'atar Abie ya kwana tare da ma'aikatansu. Koda muka shigo Galadima sama ya wuce abinsa, ganin haka Momma tace natashi na naje nima na kwanta na huta hakanan. A kunyace na mik'e domin cika umarninta. Na iske yana cire kaya, dan haka nakoma da baya zuwa falo, saida na kintaci yagama sannan na shigo, na iskeshi yashiga wanka, nima natu6e nawa na d'aura zani nasaka hijjab tareda d'aukar kayan barcina ina jiran fitowarsa. Bai dad'eba sosai kuwa yafito, sanye yake da bathtub fara tas, ban yarda na kalleshi ba natashi nashige nima. Mai makon yayi shirin barci saiya kwanta a bakin gadon a haka, k'afafunsa na k'asa, ya tsurama rufin d'akin idanu alamar yatafi duniyar tunani. Nikam ruwa mai zafi na had'a nashiga koda zanji dad'in jikina, na dad'e acikin ruwan kwance, jinakema kamar karna fito. shikansa yafara tunanin lafiya kuwa?, lokaci-lokaci yakan kalli k'ofar bayin, Amma babuni babu dalilina. Yana shirin zuwa yamin knocking sai gani nafito kuma, janye idonsa yayi daga saitin k'ofar cikeda basarwa. Ni bammasan yanayiba, dama nayi shirin barcina tun aciki, saina d'auki zani na d'ora a saman kayan nasaka hijjab nayi sallar shafa'i da wutiri, bayan na idar nad'akko roban zam-zam d'in d'aya na zauna nafara karatu Qur'an acikin ruwan zam-zam d'in. a hankali nake karatun cikin nutsuwa, dukda barcin dakecin idona. Har cikin 6argonsa da jini yakejin sautin karatuna, ya lumshe idanu yanamaijin kamar mu kwana a haka inayi. mik'ewa yayi shima yayo alwala yazo yay shafa'i da witiri yay joining d'ina muka cigaba da karatun a tare. Bamu kwanta ba saida mukayi sallar asubahi. (da yake sai zuwa 1 zasu bari ashiga wajen Abie, yau kuma babu aiki). ____((()))((*((()))*))((()))____ Yauma dai haka innarmu tadagema abbanmu saida yakira Senator Halluru agabanta, dan Zarah tana kwance babuma lafiya, ga mamansu Yaa Hameed ita kanta kallo d'aya xaka mata kagane abirkice take. Innarmu duksai suka bata tausayi, matan gidanmu kuwa abin magana yasamu, sai gulma da dariyar gatsatsa, ita kanta Momy Hadiza ta hannun damar mamansu yaa Hameed d'in dad'i takeji, tanadai nuna damuwarta agaban mamansu Yaa hameed d'inne. Bayan Abba sun gaisa da Senator halluri sukad'anyi barkwancinsu na abokai sannan yasakko xancen Zarah. Hankalin Senator halluru yatashi, danshi koda wasana baisan Zarah bata nanba, yadai lura kullum Sa'eed saiyaje gida yaci abinci, shi duk zatonsa Zaran bata iya girkine saboda ciki. Hak'uri yashiga bama Abbanmu yace wlhy shi baima saniba, amma insha ALLAH zai bincika, zuwa dare sa'eed d'in zaizo ya d'auki matarsa. Dahaka sukai sallana da Abba kowa nakuma bama d'an uwansa hak'uri akan lamarin. Innarmu bata buk'atar jin k'arin bayani dantaji komai, takumaji dad'i sosai. ()-()-()-()-()-()-()-()-()-()-()-()-()-() Jikin Abie dai kam yayi tsanani a tsakaninnan, yau kwana biyar kenan lamarin sai addu'a, dan baisanma Wanda yake a kansa ba, mai martaba Sarki Abdul'fatah ma yazo shida inno matarsa, (wannan ne karon farko dana gansu ido da ido), mutanen kirki masu d'aukar kowa nasu, duk da d'ar-d'ar danai tayi haka sukaita jana ajikinsu. yanda Galadima yake zubama inno da papi shagwa6a sai abin yaso bani dariya, amma dai sun birgeni, mu a gidanmu wazaima innaro wannan ta6arar bata k'arema uwarsa tanadiba, ba kamarma mu 'yan d'akinmu. hakama sarki jalalludden shida uwargidansa sunzo da mama Fulani. Ranar momma har tausayi tabani, kai mama Fulani batada kirki wlhy, idan kunga yanda take shinfid'a mulki a asibitin nan. Hummm🤦🏻‍♀. Galadima ne kawai maganinta, tamasa magana ya dage ya ya6a mata bak'a shikuma. Ba gidan suka saukaba, a hotel suka sauka, dan haka yau mun iskesu a asibitin sun rigamu zuwa. Tunda muka shigo mama Fulani ta zubamin ido, Galadima ya gaida mai martaba da matarsa yakoma kusada Abie ya zaina. Nima k'asa na durk'usa na gaidasu su dukansu har Momma da aunty Mimi. Momma ta nunamin kusada ita alamar nazo na zauna kusada. banyi musuba naje na zauna, dan kallon k'urillar da Mama Fulani kemin duk sai na takura. Tad'an ta6e baki sannan ta gyara zama idonta na kaina, tace “toke amarya halan saikin tashi haihuwa zaki koma mana? daga zuwa dubiya kuna Neman share wata 1 a india”. Gaba nane yafad'i, dan nafahimci dani take, saina rasa amsar dazan bata.. 'Yan d'akin kam kowa ido ya zuba ma mama Fulani har Galadima. Aunty Mimi ce tace, “Ranki yadad'e Kodai kina Kishine haka? Amarya ta kwance Miki fada wajen mai gidanki?”. Ajiyar zuciya Momma ta sauke a hankali, taji dad'in yanda aunty Mimi ta mayar da maganar wasa, ko nad'an batason abinda zai munana Munaya ko muzantata, dan bataso yarinyar taji kamar ita dabance a cikinsu......... Wani munafukin murmushi mama Fulani tayi, ta kalli Galadima da zuciyarsa tafara hasala akan tsohuwar, kamar daga sama sukaji tace, “cikin namu wata nawane Galadima?”............✍🏼 E me🙆🏻 mama Fulani mai gani har hanji🤦🏻‍♀. *_ALLAH ya gafarta na iyayrnmu😭🙏🏻_* *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻2⃣ ..............Shiru Galadima ya mata, da ace babu Momma daya ya6a mata maganar da har tabar India tana mata zafi kuwa. amma duk da haka maganar ta daki zuciyarsa, bai saniba ko zancen tsohuwarnan gaskiyane. Momma da Aunty Mimi da matar sarki kuwa kallona duk sukayi, nayi k'asa da kaina gabana Na luguden duka, saboda zancen tsohuwarnan yana son tsoratani. Shigowar Sarki Abdul'fatah (papi) da inno matarsa da mai martaba Sarki Jalaluddeen ce ta tak'aita zancen. dan daganan kowa yasaki maganar, saidai munata juyata a zukata ni da Galadima, yayinda aunty Mimi da Momma ke fatan ALLAH yasa hakane. _____________________________ Misalin 8:pm saiga Sa'eed yazo gidanmu, a time d'in gwaggon Haleematu da mamansu yaa Hameed suna ta hayaniyar fad'a, wai mamansu yaa Hameed ce takama gwaggon Haleematu tana kallon Zarah dake alwala a fanfo tana dariya. Shinefa mamansu yaa Hameed tace gwaggon Haleematu taci kanta tasha bak'in ruwa, karta lashe mata jika tun yana a ciki. Wannan kalma ta mamansu yaa Hameed itace tajawo fad'a, Dan gwaggon Haleematu tace mamansu yaa Hameed tace mata mayya bazata yardaba. Fad'a sosai sukeyi suna cin zarafin juna da gori, dama kowa kishi Na cinta a zuciya. Matan gidanmu duk sunyo waje anrasa masu dakatar dasu sai innarmu dake cewa suyi hak'uri Dan ALLAH, darene fa. Amma Sam sunk'i saurarenta. Innaro dataji hayaniyar tundaga gidanta yasata d'akko fayafi tafito, kamar anjehota haka tashigo gidan. Sa'eed da Sulaiman suna awaje a mota, duk badak'alar da akeyi daga cikin gidanmu suna jiyowa, har shigar innaro kuwa suna kallo. Dayake su Abbanmu suna masallaci. Innaro tanata magana sunk'i saurarenta, saiyi sukema kamar zasu fara danbe. Mamansu yaa Hameed Na k'ok'arin kwalama gwaggon Haleematu ludayin miya dake hannunta innaro takawo jiki zata kare sai a goshinta, jikake kwarrrr!. Tako dafe goshi tafasa k'ara.. Hakan kuma yay dai-dai da shigowar su Abba gidan, su duka ukun, tunkan sushigo sukejiyo hayaniyar dama, dukansu rai a 6ace suka shigo. Dan iskancin matan nasu ya ishesu hakanan, idonsu yarufe ko ganin motar su Sa'eed basuyiba. Ran Abba yakuma 6aci, Dan ganin duk matansa ne ma masu hayaniyar, ga abinda sukaima mahaifiyarsa akan idonsa. batareda yabi ba'asiba yace duk sufice su bar masa gida. Ananne kowa yay tsitt, yadaka musu tsawa yana fad'in wlhy idan basu fitaba zaisa a fiddasu, ko d'akunansu bai yarda wata takomaba kuma. Dole sai 'ya'yansu suka d'akko musu hijjabai suna kuka da bama Abban hak'uri. Amma yak'i sauraren kowa, daddy da baba k'arami kuwa babu Wanda yay yunk'urin hanashi. Innarmu tamatsa kusadashi tana rok'onsa karyayi haka, yazauna ya sauraresu tukunna, Hararar daya zuba matace yasata jada baya tai 6am da bakinta. Innaro kuwa maman safara'u ce takamata ta zaunar, goshi harya fara kumbura🙆🏻. (((+)))***(((+)))***(((+))) Kafin mu baro asibitin nama manta da maganar mama Fulani, saboda murnar bud'e ido da Abie yayi ta d'aukema kowa hankali kuma, gaskiya ina tausayin bawan ALLAHn nan sosai. yauma bamuyi k'asa a guywa ba wajen cigaba da addu'oin damukeyi cikin zam-zam ni da Galadima, somuke muyi na 1week sannan afara bashi. Washe gari Alhmdllh jikin Abie yayi k'yau sosai, Dan inka gaidashi yakan maka murmushin sa Na dattako, hakan ya sanya su papi sukayi shirin tafiya da yamma. Ni da Galadima da Sauban muka musu rakkiya, sainaji tamkar nabisu. Harda 'yar kwallata kuwa. Inno tanata tsokanata, Dan tsohuwar tashiga raina sosai. Tunda muka d'akko hanyar dawowa asibitin nakife kaina a cinya inata hawaye, sauban ne kawai ke tsokanata, amma Galadima tamkarma baya cikin motar. hakan saiya k'ara tunzura zuciyata, nakuma k'ara k'arfin kukan nawa. Sauban yasamu guri yay parking, da hannu Galadima yamasa alamar yaje. Fita yay yana k'uk'uni da k'umshe dariya, wai “su boss za'ayi lallashi shine aka koroni”. Saida yay nisa da motar sannan yasami damar dariyar, har yashiga wajensu Momma. Daga Momma har Aunty Mimi kalli onsa sukeyi,, aunty Mimi tace, “Auta lafiyarka kuwa?”. Saida ya zauna sannan yashiga kora musu bayani, dariya kawai sukayi, sunsan Sauban babu sauk'i wajen taso mutum agaba. Tunda Sauban ya fita sai Galadima ya gyara zamansa kawai ya zubamin ido, mutum ne shi dabaya son shiga hak'in wani, ko kad'an baiso ace wane yana cikin damuwa ta dalilinsa...... Wayarsa aka kira, ya kalli wayar kafin yakai hannu ya d'auka, salamar da akayi daga can ya amsa suka gaisa. Jin ya ambaci Nuren nagane da Wanda suka ta6a yin waya kwanakine, nad'an tsagaita da kukan ina sauraren mizasu tattauna. Galadima naji yace, “miya farune kakeson nazo Nigeria haka da gaggawa Nuren”. “no babu wani damuwa, driver da yarinyar nanfa suna hannu, so yakamata ka shigo muyi abinda yadace ko?”. “ok babu damuwa, insha ALLAH zuwa Wednesday idan jikin Abie ya kuma lafawa zan shigo”. “O right, ALLAH ya k'ara masa lafiya, a gaishesu”. “zasuji insha ALLAH, bye”. Wayar ya ajiye a tsakkiyarmu ya maida hankalinsa kaina. Cikin wani salo yace, “Munaaya!”. Wani Yarr naji a jikina, karo na biyu kenan danaji sunana a bakinsa, sainaji sunan nawa ya canja kamar ba shiba, danya iya sarrafa sunan a harshensa..... ganin ban d'agoba yakuma kiran sunan. Kasa jurewa nayi nad'ago idona na kallesa, ganin ya tsareni da idanu saina janye nawa. yad'an lumshe nasa ya bud'e a kaina ya furzar da huci “kina ganin haka abokai yakamata su kasance? ni friend nakine, miyasa bazaki iya fad'amin damuwarki ba? kiyi hak'uri nasan kina buk'atar zuwa gida, last week naso maidaki Nigeria, amma sai jikin Abie Daya motsa ya dakatar dani”. Tausayi yabani, nad'ago na kallesa, mutumne shi mai sauk'in kai, saidai idan baka fahimceshi ba zaka sameshi a amurd'e, domin yanada wahalar sha'ani, hawayen dasuka ziraromin na goge, muryata na rasa nace, “kayi hak'uri ina kewar su Munubiya ne, insha ALLAH bazan sake yin kukanba amma”. Murmushi yaymin yana jinjina kai, yad'an shafa girarsa zuwa kai sannan yace, “kinada tsiwa, amma wani time d'in kinada kirki”. Bansan lokaci da dariya tazominba, nad'an dara sannan nace kaima ai hakan kake, kanada tsauri kanada sauk'i”. Yawani k'ank'ance idanu cikin wani salon kallon yace, “really?”. Gira d'aya na d'aga masa nima nace, “yaah”. Murmushi mai k'ayatarwa yayi yakwashi wayoyinsa yabud'e motar yafita batare data sake cewa komaiba. Ganin haka nima saina fito fuskata washe da murmushi, kamar banice nagama kukan shagwa6a ba😉. Tunda muka shigo aunty Mimi da Momma suka zubo mana ido, Sauban kam dariyar shak'iyanci yafara k'asa-k'asa. Momma tace, “ina kuka mak'ale haka?”. Murmushi yayi yana zama kujerar dake kusada Abie yace, “ba ko ina Momma”.. Momma tayi 'yar dariya tace, “shikenan tunda ba'aso muji”. Sauban da Aunty Mimi ma dariya sukayi, nikam kunya tasani k'asa da kaina inad'an murmushi. __((*))__((*))__((*))__((*))__ Abba dai bai yarda su maman yaa Hameed su kwana a gidanba, a daren kowacce tanufi gidansu, yayinda baba k'arami ya d'auki innaro zuwa asibiti. Su Sa'eed kam zare jiki sukai suka koma gida, zukatansu tab da mamakin wannan lamari. A ranar zarah sai sashenmu ta kwana a tsohon d'akinmu ni da munubiya, saboda Aminu ya sanar mata yaga Sa'eed da mijin Siyama a k'ofar gidanmu. Gaba d'aya saitaji yau tanajin haushin mamansu, dan daba ta tanka dariyar da gwaggon Haleematu tamata ba ai dabasuyi rigima har Abba ya korasu gidaba, dayanzu gidanta zata kwana jikin mijinta itama, wane irin abin kunyane wannan kai kana gida uwarka na gidansu itama🤦🏻‍♀. %%%%%%%%%%%%%%% Dawowarmu kenan ni da Sauban da Samha daga zagaya gari, nagaji ovar, jikina sai ciwo yakemin, dama Yaya lafiyar giwa, saman sofa na zube Ina sauk'i numfashin wahala, wani zazza6ima nakejin yana neman rufeni, harna rufe idanu naji wayata na wringing, lalubowa nayi na duba mai kirana, nasan dai duk Wanda zai kirani to daga Nigeria ne, dan su Samha duk suna gida, Galadima kam bai ta6a kirana a wayaba, banmayi tunanin yanada number ba duk da shine ya sayi layin. Sunan munubiya dana gani yasani fad'ad'a murmushina, saida nabari ya katse sannan na kirata. Bugu biyu ta d'aga, jin muryarta can k'asa sai hankalina ya tashi, nashiga tambayarta ko lafiya. “sweetheart wlhy banajin dad'i, ko school nakai sati banjeba, ya kuke?”. “ayya sorry sweetheart, mike damunki?”. “wlhy zazza6i, kema naji muryarki wata iri ai?”. “nima lafiyar sai a slow wlhy, ina yaa marwan?”. “tofa, ciwo a time d'aya mu duka? ALLAH yabamu lafiya to, yaa marwan yafita gaida su mama, ya jikin Abie da Galadima?”. “everything Alhmdllh dear, jikin Abie ma yanata sauk'i, sun fara masa amfani da addu'oin, amma naji kamar doctors d'inshi suna complain wai abar shafa masa abinda ake shafa masa”. “karku wani sauraresu, Ku cigaba kawai, ALLAH yasa muji alkairi”. “insha ALLAH dear, dama haka Galadima yace shima”. “ALLAH ubangiji yabashi lafiya, bara na barki ki huta, a gaida minsu”. “ok sweetheart bye”. Ina ajiye wayar na mik'e, bayi nashiga nahad'a ruwa mai zafi nagasa jikina kozanji dad'i, haka nake kusan yini wanka da ruwan zafi, wai ko zan dainajin ciwon jiki, amma a banza, danayi wanka bana wuce mintuna talatin ciwon yake dawowa sabo. Wani ash d'in wando da Riga na jawo na saka, kayan basuda nauyi sosai, wandon kad'an yawuce guywata, rigar kam hannunta iya kafad'a ya tsaya, kamardai vest d'in maza take, saidai daga gaba tanada banbanci data maza. nasan Galadima bazai dawo gidan yanzuba saboda koya tashi aiki saiya biya ta asibiti kafin yazo gida, yanzu kuma akayi isha'i nasan sai zuwa irin 11, shiyyasa nayi tunanin sakasu ko zan ragema kaina nauyin jikin. komawa nayi saman sofa data zama gadona na kwanta, amma sai naji dukna takura, najujjuya naji babu dad'i kwanciyar, tsaki nayi namik'e nakoma saman gadon na kwanta, insha ALLAH kafin maishi yadawo dai natashi😏. Banfi 5minutes ba da kwanciya barci ya d'aukeni. ***** Kansa daya fara matsa masa da ciwone yasashi tattara kayansa yabaro office, Dan yau sunyi overwork ne, suna shirin fidda laptop sabon k'ira, saida yashiga office d'in vijeey da Alexander yamusu sallama sannan yanufo gida, ko asibiti bai biyaba, Dan har wani jiri-jiri yake gani a idonsa, yasan barcin dabasa samun yine ya haddasa masa ciwon kan, bama kamarshi, Dan gara ni idan yafita nakan kwanta nayi barcin. Da k'yar ALLAH yabashi Damar isowa gidan. Ko rufe motar baiyiba sai a cikin bayin ne wani yataso yarufe, a falo ya wuce Samha na barci itama, tunda muka shigo ta zube a wajen, tun yana taka steps d'in yafara cire bottom d'in Indian suit d'in dake jikinsa white color, burinsa yana shiga d'akin yagansa a gado kawai. Ganina baje a gadon yasashi yin turus yana kallona, yay saurin kauda idonsa gefe saboda kayan jikina sun kamani sosai, sun mugun fito da surar jikina d'as, gashi sun bala'in min k'yau, yau da ace matar dayake soce babu abinda zai hanashi yabawa harma yabata tukuycin wannan kwalliyar, tsigar jikinsa sai tashi takeyi, gashin jikinsa duk ya mimmik'e, rigarma yakasa k'arasa cireta, ya dafe kansa yanajan guntun tsaki, miya kawo yarinyarnan gadonsa?. Yayi maganar cikin zuciyarsa. Jin jiri na neman zubdashi a k'asa yay saurin zama bakin gadon, samu yay ya lalla6a ya ida cire kayan, duk da yafi buk'atar kwanciyar haka ya daure yad'an watso ruwa, sannan yafito yasha magani, koma shafa'i da wutiri baiyiba, a nufinsa sai zuwa anjima zai farka yayi. Abin dariya, saiya jawo dogayen filullukan gadon yajerasu a tsakkiyar gadon sannan ya kwanta can k'arshe, shima babu dad'ewa barcin yay gaba dashi. (Wlhy kafad'o babu ruwana fad'ama fans zanyi Galadima ya tik'o k'asa ehe😏🤨🤣🤣) Can cikin barci Galadima yafara juye-juye, yasaba shi kad'ai yake kwana abinsa, jin fillos a gabansa yasa hannu ya d'aukesu yayta wurgawa k'asa cikin barci, sannan yay juyi zuwa tsakkiyar gadon. Munaya kam tasaba da kwanciyar mutum biyu. dan haka ko juyin zatayi bata barin inda take kwance, duk da ma batasan da Galadima a gadon ba, tunda batasan ya shigoba. Barci yay barci saiga su yalla6ai Galadima masu jera fillos a jikin munaya😂, d'umin jikinta yasashi kuma nanik'e mata, saboda zazza6in daya rufeta, kasancewar yanajin sanyi-sanyi sai jikinta yamasa dad'i. Itama saita kuma lafe masa a jiki saboda jin sanyi-sanyi da k'amshin turarensa kuma, sunbi sun k'adandane juna kaikace ana shirin rabasune, kowa yana amfanuwa da yanayin jikin d'an uwansa. Humm, bara na lek'o su innaro 'yan Nigeria suma🤗, mai tuk'ulluma a goshi ba🤭🤫, ni nama godema mamansu yaa Hameed🤣 dama k'afar suka karya😝. _____________________________ Anbama innaro magani a wani camix suka dawo gida, gidanta aka kaita, innarmu tad'an dafa ruwa tazauna kusada ita tasaka k'aramin towel danta gasa mata goshin koza'a samu yarage tukullumar dayayi. Innaro ta 6ata fusaka zatama innarmu tijara. Baba k'arami yay saurin tareta da fad'in “haba inna, Dan ALLAH kibari tamiki, naga wad'anda suka miki abunma ko kallo baki ishesuba balle su nuna damuwarsu akai, wai shin minene laifin Ai'sha agarekine?”. Abbanmu da daddy suna zaune basuce uffanba sudai. Harara innaro tazuba ma baba k'arami kawai amma batace komaiba, itakuma innarmu ta saka towel aruwan tafara gasa mata. Tanama innarmu masifa dai har akad'an gasa mata, aikam saigashi wajen yad'an saki, baba k'arami yamik'a mata kofin tea d'in da maman fauziyya ta had'a. Kar6a tayi tana yatsine Baki, amma saigashi ta shanye tas, aka bata magani shima tasha ta kwanta. Basu bar gidanba saida tasamu barci, da innarmu tace zata kwana annan, sanin halin innaro Abba yace a'a tatashi suje gida tunda ga habiba d'iyar gwaggo safiyya dabata komaba. Badan innarmu tasoba tahak'ura, Dan aganinta innaro itama uwace agareta, kodan hallacin da mijinta yama iyayensu da darajar abbanmu, amma takula ran Abba a 6ace yake, kad'an yake jira a ta6ashi ya fashe, shiyyasa bataja zancen yay tsawoba ma. Koda suka shiga gida kowa sashensa yayi, innarmu harta kwanta saiga Abba yashigo d'akinta, abinda bayayi kenan, yakan shiga sashen matansa amma baya kwana, saidai mace tabishi nasa d'akin. Tana yunk'urin tashi zaune zata tambayesa lafiya? ya d'aga mata hannu kawai ya hawo gadon tareda janta a jikinsa suka kwanta. Bai bata damar maganaba Dan haka tayi shiru kawai kamar mai barci. Kamar yanda Abba bai isashen barciba hakama innarmu batayiba, Zarah ma kwana tayi kuka akan rashin shigowarsu Sa'eed. Hakama mamansu yaa Hameed da Gwaggon Haleematu basu rintsaba dasukaje gida. Kwana biyu da faruwar lamarin Abba yak'i cewa komai, yakuma k'i sauraren wayar da ake masa daga gidan matan nasa. Innaro harta fara samun sauk'i itama. Sa'eed kam dadynsa ya taso k'eyarsa washe gari gidanmu, an tattauna akan maganar, yafad'i dukkan abinda zarah ke masa, wani ta amsa laifinta wani kuma ta musa ba ita tayiba, sai wani cikin iyayenmu ya harareta take shiru. Nandai aka musu fad'a bayan itaba dad d'insa yace tafad'i abinda yake mata, saboda kar ahanata komawa saitace ita baya mata komai, wannan yasa aka musu fad'a da nasiha kawai akace yad'auki matarsa su tafi. Dad'i tamkar zai kar zarah kuwa, saitaji zuciyarta wasai, bata tareda damuwar komai, (kota manta uwarta bata gidansu itama a dalilinta kuma🤕?). Washe garin rana ta uku tunda safe saiga mamansu yaa Hameed tareda yayanta ya maidota, (dayake babanta ya tsufa sosai, komai nasu yanzu sai yayan nata, ko kud'inma dashi suke tak'ama yanzun, duk da mahaifinsu ya tara musu). Abba dai k'in saurarensa yayi, saida yaje ya kama k'afa da baba mai kanwa aminin marigayi mal. faruku, daddyne yamasu jagora zuwa gidan innaro dake kwance tana jiyyar goshi, damma kullum sai innarmu ta gasa mata safe da yamma, duk da masifar innaro da take sha batayin zuciyar ko nuna gazawa. Ansha fama akan Abba kafin ya sauraresu, danma akwai baba mai kanwa ne a zancen, amma ya tabbatar musu da Cewar shifa yagaji da iskancin dasuke masa a gida, tun zamanin k'uruciya har girma yafara kamasu sun k'asa canjawa, yabama kowaccensu damar k'arshe inhar suka kuma Tayar masa da rikici agida kowacce zata nemi hanyar gidansune, kuma tatafi kenan har abada, Dan bazai duba 'ya'yan dake tsakaninsuba ma. Tunda ga ranar mamansu yaa Hameed tadawo gidan, Gwaggon Haleematu kam bata dawoba, itada iyayenta sunce sai Abba yazo da Kansa koya turo anbasu hak'uri. Shikuma ya rantse saidai tayita zama inhar saiyaje bikonta. Gidanmu dai kam kwana biyu tsit kakeji, Dan baba k'arami da daddy ma summa matansu kashedi da sharad'in barin gidan gaduk wacce tasake fad'a da wata, wannan dalilin yasaka gidan yin lafiya, 'yan anguwa da makwafta sukaji kasiririt. Innaro ma ta warke abinta, saidai kam sun k'ulla da mamansu yaa Hameed, Dan yanzu ko 'ya'yanta basuda farinjini wajen innaro, ko Naziru autansu yamata Abu saita makeshi (ho innaronmu ta mutunci🤣😝). *************** Zazza6i dai yahana Munubiya sakat, yaa marwan yagaji da lalla6ata ga ciwo na cinta, yau dai yakwasheta zuwa asibiti tana kukan batason zuwa, amma yak'i saurarenta. Haka dai sukaje, bayan yankar kati dabin layi suka sami ganin doctor, gwajin farko doctor yabasu albishir d'in samun rabo na wata d'aya kacal (yaa marwan sharpshooter🤭, Munubiya dai inaga tuntu6e akayi🤫🤣). Wayyo zokuga murna wajen ogan miskilanci, babu kunya yakira Abbansa ya sanar masa, shima murna yaytayi ata cikin waya, kafin kace mi zance yabaje dangi, har innarmu labari yakai kunnenta. Harda kukan dad'i tayi, ikon ALLAH kenan, ita saida ta jera shekara 20 tana kuka da shan gori kafin ta samesu, amma ga Munubiya wata 1 da sati d'aya da aure har ALLAH ya kawo rabo. Saura munaya, k'ila itama d'indai an samu, tunda shekaran jiya dasukai waya take mata complain batajin dad'i. haka innarmu taita murnarta a d'aki ita kad'ai, babu Wanda ta sanarmawa tabarma cikinta, a cewarta idan yafita ko Munubiya tazo gidan sagani. Abin nema yasamu fa, yaa marwan tamkar zai maida Munubiya ciki, kokuma ya maido cikin nata jikinsa yarage mata wahalar laulayi haka yakeji, Dan tana d'an shan wahala gaskiya. ko girki yanzu bata iyayi balle gyaran gida. Hakanne yasaka mama rabi'a cewa yadawo da Munubiya wajenta harta samu sauk'i. Saiya fara fushi da rok'on tabarta Dan ALLAH shima zai kula da ita ai, abasu Ayusher ko feena takoma wajensu saita taimakawa Munubiya da aikin gidan. Mama Rabi'a tace a'a, Ayusher itake taimaka mata itama, feena kuwa ba cikakkiyar lafiyace da itaba, ba kowanne aiki take iya yiba ko agida (kunsan masu sikila dai🤦🏻‍♀, ubangiji ALLAH yabama dukkan masu irin wannan ciwo lafiya, ALLAH yasa yazamema rayuwarku kaffara kuda iyayenku da kullum suma hankulansu ba a kwance sukeba😢, duk mai wannan ciwon ina tsananin tausayinsa wlhy😭). Babu Wanda yaa marwan ya iya, dole ya tattaro kayansa shida Munubiya suka dawo gidan kawai, ai ko su Ayusher sunci dariya, danma fadeel bayanan, saidai a waya suka bashi labari. Munubiya tacigaba dasamu kulawa wajen mama Rabi'a, bata aikin komai saidai amata, sai idan boss nason rage nauyi ya janyeta d'akinsa da wayo ya kashe arna😉😎. Mama Rabi'a duk tana kula da su, amma saitayi kamar batasan bikin dasukeyiba, Dan taga idon yaa marwan a tsakar goshi yake😂😜. 🤥kai jama'a mu koma India.🛫⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ .................................................... ______________________________ .................................................... Zafin jikinane yafara masa yawa, dan yafara shiga sosai jikinsa, cikin barci ya laluba danson jin minene mai zafi ya rungume haka? jin kamar mutum yasashi k'ok'arin bud'e idonsa dasukai masa nauyi saboda barci, dishi-dishi yafara ganin fuskar munaya, hardai yasamu nasarar bud'e idon gaba d'aya a kanta🤫.................✍🏼 _ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🤚🏻✋🏻_ *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻3⃣ ............Shiru kawai yayi yana kallon fuskarta ta cikin d'an hasken mai kalar jaa, sai fuskar tabada wata kala data k'ara mata k'yau. yaune ranar farko dazaice yamata kallon k'urilla irin haka, yadad'e yana kallonta kafin ya janye idanunsa dake cike da barci. hannu ya mik'a ya kunna ainahin fitilar, haske ya gauraye d'akin, cikin dabara yafara yunk'urin janye jikinsa, amma tak'i yarda, saima farkawa datayi, tabud'e idanunta dasukai nauyin barci a hankali, kad'an take kallon face nashi, ta lumshe idon tasake bud'ewa. “wannan d'aurin goronfa?”. ‘galadima yay maganar a hankali cikin muryar barci, yanabin hannun munaya da ta zagaye cikinsa da kallo’. Sosai Munaya ta waro idonta yanzun, ganinta a jikinsa kwance, gashi tawani dabaibayesa saita sakeshi da sauri tana matsawa baya da waige-waigen inda take kwance. gabanta ne ya fad'i, dan ita harga ALLAH tama mance ta hau masa gado, tayi saurin rik'e kanta dake sara mata tana tashi zaune. Shima saiya tashi yana binta da kallo, a mugun sanyin murya yace “bakida lafiya ne?”. Hawaye suka wanke mata fuska, muryarta na rawa tace “kaina kamar zai tsage”. Saida yaja 1minute kafin yad'an matso kad'an, yatsunsa biyu ya d'ora gefen wuyanta, saiyaji jikin zau da zafi, ya janye ya d'aura zuwa gefen kanta, jijiyar wajen sai motsi takeyi d'ass d'ass d'ass d'ass, alamaun kan namata ciwo sosai. hannun ya janye tareda sakkowa daga gadon gaba d'aya. Ya zagayo 6ari da take, hannu yasa ya zame nata hannun data tallafe kanta dashi, ta tad'ago idanunta dake cike da barci, sunyi d'anja sun k'ara girma, idonsa a kanta, Dan haka ta janye nata ta maida k'asa tana cigaba da hawayenta. Kad'an yad'an furzo iskar bakinsa, kafin a hankali yace “mike miki ciwo bayan kan?”. Saida takuma matso wasu hawayen sannan tace, “duk jikina”. “kin fad'ine?”. Kanta kawai ta iya girgiza masa, ya cigaba da tsura mata idanu batare da yace komaiba, ganin tana hawaye duk sai yaji babu dad'i, koba komai itad'in Friend nashice ai, kamar yanda yafad'a tun farko. yad'an sauke ajiyar zuciya mai sauti kafin ya mik'e, bayi yashiga, mintuna kad'an yafito, tana a inda ya barta dafe da kanta, yace “taso kid'an watsa ruwa, ko jikin zai huce”. d'agowa tayi ta kallesa, sai taga ya tsatstsareta da mayun idanun nan nasa, tayi saurin janye nata, amma takasa tashi. matsowa yayi kusada ita, ya mik'a mata hannunsa, alamar takama ta tashi, ta d'ago ta kallesa ya d'aga mata kansa yana mai lumshe idanunsa alamun tabbatarwa. Hannunta ta saka a cikin nasa, ya had'e waje guda sannan ya taimaka mata ta tashi tsaye, kallo d'aya yamata ya kauda kai, dukda kayan nata masu kaurine saida yaji wani Abu daban, dansu fidda surarta sosai. Har wajen wankan yakaita, sannan yafito batare da ya ce uffanba. da kallo tabi bayansa, a ranta tana mamakin sauk'in kai irin nasa, ada kallon mutum mai girman kai take masa, amma tunda suka fara rayuwa a tare saita fara fahimtar ba haka baneba, kawai dai shi mutumne dabai cika hayaniya da surutu ba, shiyyasa inbaka gama saninsaba saika dunga masa kallon mai girman kai. Koda ya fito saiya had'a mata tea, shi dama baya rabo dasu a d'akinsa, magani ya d'akko shima ya ajiye, yakoma bakin gadon ya zauna yana tsumayen fitowarta. Kusan mituna 10 tagama watsama jikinta ruwan, lallai naji dad'i sosai, saidai kuma bazan iya maida kayan dana cireba, inajin kunyarsa, kuma jinsu nake sun d'auki zafi, towel naja Na d'aura, saidai bashida girma, bazan iya fita a haka dashiba Galadima yana d'akin, kad'an nabud'e k'ofar Na lek'oda kaina, yad'an juyama k'ofar bathroom d'in baya kad'an, a hankali cikin muryata mai nuna alamun banida lafiya nace “please yalla6ai ka taimakeni da hijjab”. Waiwayowa yayi ya kalleni, alamun baijiba sosai, Na turo baki kad'an sannan nace “please yalla6ai hijjab”. Baice komaiba ya mik'e, inda nake ajiye hijjab d'in yaje ya d'ako, yazo inda nake ya d'oramin akan hannuna dana mik'o, kallon ido cikin ido mukaima juna, kowa ya janye cikeda basarwa. Bayan nasaka hijjab d'in nafito kamar wata muna fuka, sai k'asa nakeyi da idanu nakasa kallonsa, shima idonsa a lumshe ya jingina da fuskar gadon, wucewa nayi wajen akwatina Na d'akko wasu kayan barcin, bayi nakoma Na saka, saina yafo k'aramin Vail Na cire hijjab d'in. Yabud'e idanu kad'an a kaina, batare da yayi magana ba ya nunamin mug d'in daya had'a tea a ciki. nad'an yatsine fuska da marairaice murya tamkar xanyi kuka, “ALLAH yalla6ai banajin yunwa”. Shiru yay kamar bazai tankaba, saida yaja kusan 2minutes sannan yatashi zaune sosai, batare da yayi magana ba ya d'auki mug d'in da drug's d'in ya taso inda nake zaune a kan sofa, saman k'aramin table d'in gaban kujerar ya zauna yana fuskantata, d'an gaf d'in daya bari tsakanina dashi bai wuce tafin hannuba, Dan har inajin saukar numfashinsa, baya nad'anja kad'an Na jingina da jikin kujerar, amma hakan bai hana kusanci sosai tsakanina da shiba. babu magana babu komai naji dirar cup a bakina, d'ago ido nayi tamkar zan fasa kuka, danni wlhy banajin shan shayinan, yamin hararar data saka 'yan cikina harmutsawa, babu shiri nabud'e baki na kar6a, ya had'e girar sama da k'asa, baibar ko k'aramar k'ofar dazan kawo masa wargiba, haka naita kar6a ina hawaye, saida yaga Na shanye tas sannan ya barni yana hararata, nidai yau babu k'arfin mayarwa, yabani maganin, shikam babu musu Na kar6a nasha. ganin yanda naketa hawaye saiya zubamin ido kawai yana kallon ikon ALLAH, nikam banida niyyar daina kukan nawa, kuma nima bansan dalilin kukanba, kawai dai jinake hawayen Na tahowa. Ya zuba tagumi abunsa yana kallona kamar yasamu television. kallon dayake min saiya k'ara tunzurani, nafara kuka mai sauti harda shashsheka. Tagumin yacire yana wani k'asaitaccen murmushi, ya mik'e tseye yakoma kan gadon, filolin dasuke k'asa ya d'auka ya jera a tsakkiyar gadon kamar d'azun. nidai duk ina kallonsa, saida ya lullu6ama k'afafunsa bargo zuwa cikinsa sannan yace, “taso ki kwanta sarkin arhan hawaye”. Harara Na zuba masa batare da Na shiryaba, sai kawai ya ta6e bakinsa yay kwanciyarsa ya barni, tareda kashe fitilar ya maida ta barci. Kusan mintuna 4 Na zame Na kwanta a kujerar, amma sainaji duk babu dad'i, saboda maganin bai fara tasirin da jikina zai bar ciwonba, tashi nayi nakuma zama, kusan 5munutes sannan natashi sad'af-sad'af tamkar munafuka na haye gadon. Ni duk tunanina yayi barci. Ashe duk abinda nake yanajina da kallona. murmushi yayi kawai yana lumshe idonsa, a ransa yana jinjina irin rashin wayona. Ajiyar zuciya Na sauke a hankali, sannan naja bargon dayake babbane Na lullu6a, mintuna kad'an nafara zufa, alamar zazza6in ya sauka. Bargon na janye don insha isaka, bansan sanda barci ya saceni ba. Juyowa yayi ya kalleni, yaga ina sauke numfashi a hankali alamar nasamu barci, k'aramar ajiyar zuciya ya sauke kafin yasake addu'a shima ya gyara kwanciyar sa. ★★★★★★★ Yau gidanmu sun tashi cikin tashin hankali, Abbah yay Accident yayin dawowa gida daga wajen aikinsa, innarmu Na kwance ciwon kai dukya isheta, tunda ta tashi da safe dashi ta tashi, gasu Aryaan sun isheta da ihun fad'ansu, sai mugun wasa sukeyi suna guje-guje a falon, amma takasa d'aga kai ta tsawatar musu. Zuciyarta cike da kewar su Munubiya, inda suna nan da yanzu suke bata taimako, koyaya tace batajin dad'i zasu rud'e, amma gashi yau ko wanke-wanke tama rasa mai matashi, sai Zainab maman fauziyya tasaka tayi mata, amma 6angarenta ko shara bai samuba yau, kuma tun d'azun tafara jin mamansu yaa hameed tana k'ananun magana akan tak'i fitowa ta aza musu girki, maimakon sunga shiru su lek'o suji ko lafiya? A'a su babu ruwansu, kawai a dafa abasu suci da 'ya'yansu... Wayarta dake ring ta katse mata tunani, ta kalli su Aiyaan dake danbe Aryaan Na kuka saboda dukansa da Aiyaan yayi a baki. “wani cikinku ya d'akkomin wayata saman freight”. Cikin kuka Aryaan yace “Innarmu kingafa ya dokarmin baki”. “kukuka Sani, nidai nace wani ya d'akkon waya acikinku, idan kuma kuka bari Na tashi sai jikinku yagaya muku”. Aryaan ya d'akko mata wayar ya kawo mata, lokacin harta tsinke, ganin Abbanmu ne yasata bin kiran, bugu biyu aka d'aga, ko gaisuwa bai bari sunyiba, yace mai wayarne yayi Accident, yanzu haka suna general hospital. “innalillahi wa'inna'illaihirraji'un” innarmu tafad'a tana mik'ewa zumbur, ga wata zufa Na karyo mata, batasan tayo waje tana kwalama matan gidan kiraba. Kowacce tafito jiki Na 6ari, azatonsu wata acikinmu aka sako, musamman ma ni dasuke kiran aurena auren d'ori d'afini. tana hawaye ta sanar musu da abinda yafaru. Nanfa gidan ya rikice, yara suka garzaya suka sanarma innaro. Ko takalmi babu haka tanufo gidanmu tana shar6ar majinar kuka da kiran tashiga uku, Awwalu zai mutu ya barta. wannan kwakwazon natane ya ankarar da jama'ar anguwarmu. A rikice baba k'arami da Dady suka nufi asibitin, Dan matan gidanmu sun kira suma sun sanar musu abinda ke faruwa. Kafin wani lokaci jama'ar gidanmu sun gama cika asibitin, sai koke-koke sukeyi suna son ganin Abba, amma an hanasu, Dan bak'aramin buguwa yayiba. ______________________________ Alhmdllh natashi jikina da sauk'i, Dan kuwa babu zazza6in da ciwon jikin, hakama ciwon kan babu, bai tadani ba saida yadawo massalaci, lokacin har gari yafara haske ma. Na idar da salla ina zaune ina addu'a yafito daga bathroom, da alama wanka yayo, Dan sanye yake da bathrobe sky blue, yana rik'e da k'aramin towel a hannu yana goge ruwan fuskarsa. Kallo d'aya namasa Na d'auke kaina, shikoma bai kalleni ba ya wuce gaban mirror ya zauna, saida yafara shafa mai sannan Na tsinkayo muryarsa yana fad'in “ya jikin naki?”. Yanda yay maganar a cinkushe yasakani d'agowa Na kallesa, ganin hidimarsa kawai yakeyi saina d'auke kaina, nace “da sauk'i”. Bai sake magana ba, harya kammala yabar gaban mirror d'in, wajen wardrobe yakoma, nidai kaina Na k'asa bansan hidimar dayakeba. Koda ya d'auki kayan saiya koma bayi ya saka tamkar yanda ya saba, ya fito ya iskeni ina gyaran gadon, ta gefen ido Na kallesa, yayi k'yau cikin wani bak'in lallausan yadi, Wanda akaima ado da jan style, nakula yanason kayan al'adarsa, dukda baitashi ya girma cikin k'abilar tasaba, sock's ya d'akko da bak'ak'en takalma sau ciki ya zauna saman sofa, yana sakawa yana magana, “uhm Zanyi wata 'yar tafiya Na kwana 2 kacal, mikike da buk'ata?”. Tsayawa nayi daga gyaran gadon danake, Na d'ago ina kallonsa kawai, jin nayi shiru kuma yanajin alamun ana kallonsa ya d'ago shima. Ido muka had'a saina janye nawa. “kallon fa?”. ‘yafad'a yana k'ok'arin saka d'ayan takalmin’. Cikin la6e baki nace “yoni yalla6ai mizan kalla anan?”. Banza yamin, saida yagama saka takalminsa sannan yamik'e tsaye yana fad'in “hakanefa, Ashe babu abin kallo anan”. Nima shiru namasa ban tankaba, ya saka laptop d'insa dawasu 'yan abubuwa a k'aramar briefcase d'insa, ya zuge zip d'in yana fad'in “ki shirya muje kiga likita kafin Na wuce”. Da sauri nace “a'a kaje abinka, Indai nice Na warke”. Idanu ya tsuramin alamun tuhuma, nikuma nak'i kallonsa, ya girgiza kansa kawai sannan ya ajiye min kud'i akan gadon, “ni Na tafi, a yafi juna”. 'Dagowa nayi ina kallonsa da mamakin kalmarsa ta k'arshe, bansan sanda bakina ya su6uce nace “ALLAH ya tsare hanya, ya dawo dakai la fi ya”. ‘na k'are maganar da d'aid'aya’. Cak ya tsaya abakin k'ofar, saboda yanda addu'ar tawa tazo masa a bazata, dan bai tunanin hakan daga gareniba, yajuyo a hankali tamkar maison gaskata abinda yaji, kallona yayi muka had'a ido, amamakina saiya sakarmin wani tsadajjen murmushi, irin Wanda zan iya rantsuwa ban ta6a gani daga garesaba. Baice komaiba yajuya yafice da sauri. Yabar zuciyata da luguden dabansan dalilinsa ba. Wata ajiyar zuciya Na sauke, tare da zama jagwaf a bakin gadon na dafe kaina da mamakin murmushin da Galadima yamin. Bai dad'eba sosai a hospital yamusu sallama yafito, dama tun a daren jiya ya sanar musu zaiyi tafiya, ga jirgi kuma ya kusa tashi. yafito sunata binsa da addu'oin dawowa lafiya, yayinda shikuma yake amsawa cikeda murmushi. Saida yafara xuwa sukayi magana da doctors d'in dake kula da Abie, yaji babu wata Matsala sannan yafito. Dama Khumar ne ya kawoshi, Dan haka yanzu ma shine yatafi kaisa airport d'in. Zaman da baifi 30minutes ba jirginsu yataso zuwa 9ja. Zaune yake kusa da window, yayinda wata matashiyar budurwa ke gefensa, tunda tazo da nufin zama yawani kuma had'e fuska, a d'age ma ya amsa mata sallamar data masa, yasaka belt tareda bud'e Newspaper yahau karatu. Budurwar sai satar kallonsa takeyi, tanason masa magana amma bataga fuska ba. Sai da akazo tambayar misuke buk'ata?, yace Coffee. Itama da sauri tace Coffee d'in. juyowa yayi ya kalleta, ta sakar masa wani tsadajjen murmushi. Janye idonsa yayi yanajan tsaki a zuciyarsa. duk yanda taso yamata magana ko sau d'ayane Galadima yak'i yayi, ya had'e gabas da yamma abinsa. Haka kawai sai tunanin tahowarsu da Munaya ya fad'o masa a rai, yatuna yanda tadinga wani dakewa irin itafa ta saba da hawan jirgi. jaridar yasaka ya rufe fuskarsa yana murmushi da jinjina jan aji irinnan yarinyar, ita bata yarda aga marenarta ba. ya tuna diramarsu ta daren jiya, wani murmushin yakuma saki...... haka abubuwa da yawa sukaita dawo masa akan Matar tasa ta auren Contract. wani abun nata abin dariya, wani Na mamaki, ita bata yardaba adole big girl Ce. Koda suka sauka baiko kalli inda yarinyar nan takeba, da sauri tabi bayansa tana fad'in “haba yayana babu sallama? Ai kodan darajar makwaftaka mayi sallama”. Yana sauka daga step d'in k'arshe Na jirgin ya juyo ya kalleta, aransa yace yarinya sai nacin jaraba. Ta kuma fad'in “kozaka bani Number ka muke zuminci”. Yanzu kam wata uwar harara ya zuba mata kafin yay gaba abinsa. tsaye tayi tana binsa da kallo, jitake kamar ta tsala ihu, harma tafara tunanin ko shid'in kurmane?. cikin matuk'ar mamaki ta hango wasu masu kaya iri d'aya sunyo wajensa, daka gansu kaga jama'ar masarauta. da k'yar ta had'e yawun bakinta, kenan shid'in jinin sarautane?. Batada mai bata wannan amsar, Dan haka taci gaba dabin motocin Galadima da kallo har suka fice abinsu. Driver d'in da yazo d'aukarta yak'araso inda take, gaisheta yafarayi kafin ya k'ar6i handbag d'in hannunta. amota take tambayarsa koya San wanene Wanda masu kaya iri d'aya sukazo d'auka?. Yace, “ma'am Galadima Sameer kenan, d'an tsohon Sarki, kusan 1month kenan da aurensa ai”. Hararsa tayi cikin daka tsawa tace “ina ruwana dawani aurensa, bashi Na tambayeka ba. Punishment d'inka Na fad'amin abinda ban tambayeka ba shine ka nemomin number sa”. “ALLAH ya huci zuciyarki Ma'am”. Banza tamasa, yayinda shikuma zufa keta karyo masa dukda AC n dake motar, tunaninsa a ina shikuma zai Samo number babban mutum irin Galadima Sameer shikam? yasan idan bai samo d'inba yashiga uku, dan yarinyar nan ba mutunci gareta ba. ********************* Tun bayan tafiyar Galadima saina zama wata sukuku, abin mamaki saigani da kewar Galadima wai, gaba d'aya yinin sai nayishi wani babu dad'i, ga gabana yanata yawan fad'uwa, jinake kamar wani al'amari yana shirin faruwa da rayuwata. Sauban ma sarkin tsokana kasa shiru yayi saida yay magana. Bayan ya dawo school sai muka tafi asibiti, tunda Na gaida Abie da Momma da Aunty Mimi saina koma gefe nayi shiru abina, ciwon jikine kawai ke nuk'urk'usata, dan ga6o6ina masifar ciwo sukemin, narasa wannan dalili? zazza6inma banaji yanzun, ga yawan fad'uwar gaban dana yini inayi, sai kasa kunne nake naji ko Galadima zai kira wani a 'yan uwansa yace ya sauka lafiya, dan zuciyata tafi karkata da fargaba a kansa. Shirun da Sauban yaga nayi shine ya kalleni yana dariya k'asa-k'asa. “Aunty gimbiyarmu har kin fara kewar Hubbin naki halan?”. Idanu nad'an waro ina kallonsa, ganin su Momma Na dariya saina 6oye face d'ina cikin veil d'ina ina fad'in “kai yaa Sauban ALLAH a'a”. Dariya suka kuma sanyamin, Abie nata murmushi shidai, Momma tace, “A'a Mrs Galadima kifad'a gaskiya dai?”. Kunya takuma lullu6eni, saina k'udundune kaina gaba d'ayama a gyalen saboda. ina k'aunar wannan family sosai a raina, saboda nima suna nunamin tsantsar k'auna, ko yau nabar cikinsu auren contract d'inmu yak'are bazan manta da alkairinsuba a gareni. Haka nagama shirin barci Na kwanta a gadonsa ina shak'ar k'amshin turarensa danakejin dad'insa fiye da da. nadad'e ina juye-juye banyi barciba saboda damuwace cinkushe da raina, ga zazza6i mai zafi ya rufeni, bansan ina Galadima yajeba balle nayi tunanin samun number na kirashi, Na gwada number shi ta nan India tak'i wucewa, dama a wayar Samha Na d'auki number bama ta saniba, yau babu mai kulawa dani, sainaji wata kewar innarmu da Munubiyata sun dawomin sabo fil a zuciya. Sai da dare yakusa rabawa kafin barci mai nauyi ya d'aukeni. _____ .★. _____ .★. _____ Har yamma ba'abari kowa yaga Abba ba, 'yan gidanmu sunci kuka harsun gode ALLAH, Su Munubiya da dukkan yaran gidanmu Na ma'auri tuni labari ya iso musu, kuma duk sun tattara a asibitin suma. Doctor d'in dayake kan Abbanmu ne yafito yana basu hak'uri akan suje gida hakanan, dan gaskiya baza'a bari suga Abba ba a yau. Sabon kukane yatashi, musamman ga innaro, idan ka kalleta dolene tabaka tausayi wlhy, yau babu jarabarnan da rashin mutunci, kuka take da fad'in Auwalu karya tafi ya barta.......... Sambatunta yakuma raunana zukatan mutane da yawa a wajen. Munubiya tayi yunk'urin kirana amma network yahana, da Yaa marwan yakula da hakan kuma ya hanata, yace karta sake ta sanarmin yanzu. Wannan dalilin yahana a sanar min d'in. Kowa zuciya babu dad'i suka tattara suka tattafi gida, dady da baba k'arami, yaa hameed yaa shafi'u da ya Naseer aka bari a asibitin zasu kwana. Ranar duk Wanda yasan gidanmu yasan babu lafiya, Dan gidan yayi tsitt, kowa tashi ta isheshi a zuciya, barcima k'alilanne daga cikinsu suka yisa. ___________________________ Sosai hadimansa sukayi farincikin ganinsa, kamar yanda shima yay farin cikin ganin Nasu, sud'in mutanene masu muhimmanci a rayuwarsa, sunzama wasu 6angare na duniyarsa. Kwance yake a bayan motar idonsa a lumshe, ya saki guntun murmushi saboda tinano yanda zata k'are masa a wajen Momma, koda wasa bai sanar mata Nigeria zai zoba, yayi hakane kuma dan kartayi yunk'urin dakatar dashi ma. jin alamar motar ta tsaya ya bud'e lumsassun idanunsa tareda furzo k'aramar iska, duk da isowar dare yayi hakan baisa sauran hadimansa sun kwanta ba, ya iskesu zazzune a k'ofar sashensa suna jiran isowarsa. Dogarin daya bud'e masa k'ofar yafara k'ok'arin d'aukar briefcase d'insa domin shigar masa. Shima ziro k'afarsa d'aya yayi ta inda aka bud'e masan, ya zuk'i iskar masarautarsa tareda fesota tabaki yana lumshe idanunsa, ko ina kwanyar yake da hasken lantarki tamkar rana, duk lokacin daya zo cikin masarautarsa, mahaifarsa, yakan tsinci kansa cikin tunano abubuwa masu d'aci da rad'ad'i a zuciyarsa, yakanji inama ace shid'in ba kowa baneba, inama ace shid'in talakane fitik mai tarin kwanciyar hankali, da za'ace yaza6i rayuwar dazaiyi, da zai za6ama kansa zama talakane, dan babu Wanda yakai talaka kwanciyar hankali inhar yanada k'yak'yk'yawar zuciya da wadatar zuci, amma babu komai a cikin dukiya da mulki sai damuwa darashin kwanciyar hankali, kai kenan kullum cikin rashin nutsuwa, idan kayi wasama ibadar da ubangiji ya halicceka dominta bazakayiba, ya had'iye wani Abu mai d'acin gaske a mak'oshinsa. sannan yashiga k'ak'aro murmushin dole ga sauran hadimansa dake gida basuje tarbarsaba. daka kallesu kasan suna cikin tsantsar farincikin ganinsa, dan sunyi kewarsa, shima hakance agaresa. bayan sun gama gaggaisawa ya tambayesu lafiyarsu sannan yashige ciki. Ko ina k'al yake tamkar yanda yake buk'atar ganinsa, (hadimansa nada k'ok'arin tsaftace sashensa koda baya k'asar). Zama yay bisa kujera yana fad'in “ya ALLAH! Alhmdllh”. Dogarin daya shigo masa da jakka yakuma masa sannu da zuwa sannan yafice. Yakai mintuna 5 a wajen zaune, sai k'ullawa da kwancewa kawai yakeyi, ga gajiyar zaman jirgi na nuk'urk'usarsa data rashin isashen barci dabasa samu shida Munaya. da k'yar dai yamik'e zuwa bedroom d'in, komai need sai k'amshin mayen turarensa da air fresheners mai sanyin dad'i ke tashi, ya ajiye jikkarsa a kan gadon sannan yafara zame kayansa danya samu ya watsa ruwa. Ya d'an jima a bayin sannan ya fito d'aure da towel, yana tsane fuskarsa zuwa kai dawani. wardrobe yabud'e ya d'akko boxes kawai yasaka, sannan ya saka jallabiya, sallolin da suka riskesa a hanya ya rama, yana idarwa yacire jallabiyar, matsawa yay jikin mirror ya fesa turare kad'an ya hau gadonsa da yay missing. harya kwanta yatashi zaune, briefcase d'in dayazo da ita ya bud'e, ya Ciro wayoyinsa tareda layinkansa na Nigeria duk ya saka, sannan ya ijiye wayoyin, insha ALLAH zuwa lokacin da zai tashi yana fata komai ya dai-daita. Addu'ar barci yayi ya gyara kwanciya, amma sai barci yace bai gadaba, tunanin ahalinsa daya baro wata k'asa ya dabaibaye zuciyarsa, wata kewarsu ke tsikarar zuciyarsa, yanzu yasan Abie yayi barci, hakama Momma watak'il ta kwanta, dan macece mai yawan k'iyamull laili, duk da a asibiti takan kwana hakan baya hanata kusanta kanta ga mahaliccinta, Aunty Mimi da Samha ma yasan sunyu barci, Sauban ne dai dakamar wahala ace ya kwanta, ya juya kwanciyar sa yana murmushi, zuciyarsa tace “to matar contract fa?”. ya d'age kafad'a da ta6e bakinsa kad'an, saikuma yasaki k'aramar dariya, daren jiyane kawai ya fad'o masa a rai, yau kuma koyaya ta yini ta kwana? (danba time d'inmu d'aya da India ba), a fili yace, “ALLAH yasa yau dai babu zazza6in, my Friend kin cika taurin kai, dakin yarda nakaiki asibiti zanfi samun nutsuwa, oh god🤦🏼‍♂”. ‘ya k'are maganar da dafe kai’. Shima yajima baiyi barciba, sai can dare yaja da nisa sannan ya saceshi. Da asubahi da k'yar ya iya tashi, alwala yay yafita massalaci, bayan an idar da salla yafito suka had'u da Sarki da jama'a keta zubewa suna kwasar gaisuwa. Sarki yayi mamakin ganinsa, dan har saida fuskarsa ta nuna hakan, murmushi kawai Galadima yayi yana rissinar da kansa k'asa. Sarki baice masa komaiba yanufi sashensa, sai Galadima yabi bayansa, dogarai kuma suka take musu baya, bayan sun gaida Galadima d'in. A hamshak'in falon mai martaba na farko suka yada zango, Sarki na zaune bisa kujera mai zaman mutum biyu, Galadima na k'asa kusada k'afafunsa. Kukun Sarki ne suka shigo shida jakadiyya bayan sunyi sallama.. K'aramin tire suka ajiye dake d'auke da butar shayi, sai mug da wani k'aramin bowl mai k'yau anzuba sukari, sai jug k'arami shima an zuba tataccen lemon tsami, saikuma Zuma shima a k'aramin bowl. Kuku da jakadiyya suka zube gaban mai martaba suna kwasar gaisuwa, sannan suka gaida Galadima shima da masa barka da zuwa. Cikeda kulawa ya masa musu, har kuku ya durk'usa zai had'ama mai martaba shayin Galadima ya dakatar dashi, tareda masa nuni dayaje abinsa. Kuku ya rissinar da kai alamar girmamawa sannan suka fice shida jakadiyya suka basu waje. Galadima ya had'ama Mai martaba shayi da ruwan lemon tsami kamar yanda yasan yana sha a kowacce Safiya, (ada mahaifinsa yasani da wannan al'adar, dan awajensa Sarki jalaludden ya koya). cikeda girmamawa ya mik'ama mai martaba mug d'in, kar6a yayi yana masa murmushi, sannan yace “kaifa?”. Girgiza kai Galadima yayi, yace “a'a Abba, wannan sai ku”. Mai martaba yay murmushinsu na manya sannan yace “Saukar yaushe Sameer?”. Galadima yad'an shafa wuyansa, cikin tsantseni yace, “da daddare Abbah, wani business ne ya kawoni, inaga insha ALLAH zamu bud'e company anan Nigeria saboda muma matasanmu su Mora daga guminmu”. Murmushi mai martaba yayi, ya kur6i shayinsa sannan yace “tunani mai k'yau yarona, ALLAH yasaka hannu a lamarin. ya jikin d'an uwana dasu auntyna Zeenah?”. “jikin Abie Alhmdllh Abba, dan bayan tahowarku sauk'i yakuma samuwa gaskiya, Momma kam suma lafiyarsu lau”. “to Masha ALLAH, tareda iyalin naka kazo kenan?”. “a'a Abba, ni kad'ai nazo, saina kammala abinda nazoyi itama idan zan dawo zamu dawo tare”. “to ALLAH ya tabbatar”. “Amin Abba, bara naje nad'an kimtsa mu gaisa da jama'a, dan zan d'an fita”. “ok, ALLAH yayi Albarka”. “amin Abba, a huta lafiya”. Hannu kawai mai martaba ya d'aga masa, Galadima kuma yafita. Babu inda ya Shiga, ya koma sashensa domin yayi shiri. saida ya had'a coffee da kansa kamar yanda ya saba idan yazo k'asar, ya zauna yasha danba abincin kowa yakeci a masarautarba, ko Ummu hasheem bayacin abincinta kota kawo, duk da kuma kulawa datake nuna masa fiye da kowa a gidan, gimbiya zulfah uwargidan sarkima tanada k'ok'arin aika masa abincin inhar yazo, amma ko kallon kulolin ma bayayi, saidai bayinsa su cinye. Yafito wanka yana tsane jikinsa wayarsa tayi k'ara alamar shigowar sak'o, wayar ya d'auka danya duba ko company ne, dan yana fatan ace komai ya daidaita ne, yanason kiran su Momma yaji Yaya jikin mahaifinsa. Ganin number ce sai abin yabashi mamaki, bud'e sak'on yayi kawai azatonsa ko Nuren ne. _Gargad'i!! tabbas sirikinka ya tsira a wanan karon, amma ka tabbatar masa next time bazamu barsaba, saimun raba ruhinsa da gangar jikinsa!!!!.................._✍🏼 *_ALLAH ya gafartama mahaifanmu😭🤚🏻✋🏻_* *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻5⃣ ..............Bayan an idar da salla Galadima yace wanne office yakamata su fara zuwa?, mtn ko glo?. Shiru Nuren yay yana tunani, zuwa can ya kalli Galadima “Sameer mizai hana mubari sai zuwa gobe, kasamu kaje kad'an kwanta ka huta, kaga yanda idonka yay jazur kuwa, ga jijiyan dukta tashi”. Lumshe idanu Galadima yayi yana furzar da huci mai zafi a bakinsa, “Nuren muje kawai, kona kwanta bazan samu nutsuwa ba, kaga fa yanda suka jigata bawan ALLAHn nan”. “hakane, amma karka damu muje kai dai kawai”. Galadima bai musaba, suka jera shida Nuren zuwa wajen mota, bayan anbud'e musu sun shiga sai Nuren yacema Sarkin mota suje hotel d'in daya sauka. Galadima yanajinsu amma baice uffanba, yayi shiru kawai yana kallon jama'a ta glass. Koda suka isa hotel d'in sai Nuren yace su sarkin mota suje abinsu, zuwa anjima zai kirasu su maida Galadima d'in gida. Cikin girmamawa sarkin mota ya amsa da to, yamusu sallama suka tafi. Koda suka isa d'akin da Nuren ya sauka Galadima cire rigar shaddar yayi ya kwanta dagashi sai dogon wandon da vest, kwanciyar mintuna 5 kacal barci yay gaba dashi. Sosai tausayinsa yakama Nuren, yanason d'an 'yar uwar mahaifinsa sosai, (Nuriddeen d'ane ga Abubakar yayan Momma, babban d'an Sarki Abdul'fatah daya gaji sunan Sarki Abubakar kakansu Galadima, mahaifin Nuren ayanzu haka shine mai jiran gado a masarautar su momma, Nuren d'ansane na biyu, akwai yayansa Ballo, shid'in sa'an Galadima ne, kusanma tare akayi goyonsu, amma Galadima ya girmesa da watanni 7 a duniya, kunga d'an uwansane na jini kenan, ta 6angaren mahaifiya👌🏻). Galadima ya jima yana barci, dan kiran sallar la'asarne ya tadashi ma, wanka yasake yi, ya kar6i kayan Nuren ya sanya, k'ananun kayane amma sun masa k'yau sosai, Nuren nata tsokanarsa, wai kayan sun masa k'yau, inhar Munaya ta gansa bazata ganeshi ba. Harara ya zubama Nuren, sannan yanemi hanyar fita, “malam idan kagama surutun saika taho muje”. “sorry sarkin gagara badau mai jiran gado”. tsaki Galadima yayi kawai yafice abinsa, shifa haushin mai jiran gado d'innan yakeji idan aka ambata masa, sadai nemi mai jiran gadonsu amma bashiba, mtsoww!!. Wata mota dake fake a harabar hotel d'in suka nufa, Nuren ya zauna a mazaunin driver, yayinda Galadima ya zauna gefensa. A hankali Nuren ke tuk'in suna 'yar hirarsu jefi-jefi, dayake kowanne akwai nutsuwa basuda yawan hayaniya, dan shima Nuren d'in bashida surutu. Tafiya mai d'an nisa ta kaisu wani k'auye, bawani babban gari baneba can. Galadima ya kalli Nuren yana hararsa, “wai Nuren bazaka saida gidannan ba dai ko?”. Murmushi Nuren yayi, yad'an gyara zamansa yana kallon Galadima, saikuma ya maida ga hanya. “brother kenan, ai yanzu ba abinda kuke tunanin nake aikatawa ba a gidan, wlhy babu ruwana da 'yar kowa yanzun”. “Humm Nuridden! nasan inhar kana tareda Muzaffar bazaka ta6a daina neman mataba, nidai bazan gaji da gaya maka gaskiya ba, inhar aure kakeso kawai kayi aure, bazaka gane llar zina ba saika auri yarinyar da wani yagama Sani, saika haifi yara kuma, Nuren! Ba cika baki nakeba, bakuma nafi k'arfin ALLAH ya jarabceniba, amma dana aikata zina ka ganni nan gamma a d'auramin aure da mata hud'u a rana d'aya, please and please d'an uwana, ka canja tun Kannada damar hakan, dukkanin ahalinmu basa son wannan d'abi'ar taka wlhy”. Nuren ya jinjina masa kai yana cije la66a, “na gode d'an uwana, insha ALLAH nabari har abada, kuma kwannan zakaji maganar aurena ta tashi, wlhy tun wancan lokacin da abunnan yafaru ban sake mu'amulla da kowacce maceba, idan najima zan takura saina fara azumi”. “tom ALLAH yacigaba da gadinmu muda zuciyoyinmu, amma Auren shine tafi cancanta dakai, dan wani lokacin da mutum yakai azumin ma zakaga komai yadawo, kaga Auren shine cikakkiyar mafita kawai”. “gaskiyane wlhy, ALLAH dai ya k'ara shiryamu”. ‘Nuren yafad'a yana horn a k'ofar gate d'in katafaren gidan gonarsa dayake kiwo’. An bud'e musu gate d'in suka shiga, ma'aikatan sai murnar ganinsa sukeyi, tsayawa yay da motar batare da sun fitoba, sukaita zuwa gaishesu, bawani Sanin Galadima sukayi sosaiba, tunda bawani zuwa wajen ya keyiba, Nuren zai fad'a musu wanene, amma Galadima yamasa nuni da karya fad'a, hakkane yasakashi 6ame bakinsa. ****************************** Ran mama Fulani a 6ace yake kallon manyan jikokin nata maza guda uku tayi, cikin isarta da k'asaitarta tafara kiran sunayensu, “Talba! Wanbai! Matawalle!, kunsan dalilina Na taraku anan kuwa?”. A tare suka girgiza mata kai kawai. Takuma gyara zamanta cikin tsantsar mulki da izza, tace, “nakula mahaifinku har zuwa yanzu baison ciwonku ba, shi dole yanaso ace masa adalin Sarki, shiyyasa kullum yake fifita d'an wani bisa Ku da ALLAH ya bashi, Matawalle shekarunka dana Galadima kusan d'ayane, amma mahaifinku nagani Galadima yay aure bai ta6a nuna damuwarsa akan kai kayiba balle sauran 'yan uwanka, to yanzu matar Galadima cikine da ita, kuma tabbas ta haifi namiji kuda sarautar gagara badau saidai kallo”. A razane Talba da wambai suka zaro idanu waje a zabure, matawalle kuwa murmushi kawai yayi yana girgiza kai da mamakin wannan kakar tasu mai shegen son kanta. Wambai yace, “haba Granny miyasa kike fad'ar wannan maganar, yakamata bakinki ya fad'i alkairi mana, shi dan uban cikin basai mun bari an haifesa ba, koshi uban cikin dayake tak'ama yana jiran gado bai isa yayi mulkiba balle cikin da babu tabbas d'in haifosa, ni wlhy kinma 6atamin rai”. Talba yaja tsuka shima yana harare-harare, “Granny ya akayi kikasan tanama da cikin to? wannan sarkin girman kai d'inne zai iyama mace ciki?”. Harara mama Fulani ta zubama Talba, “to uban matanbaya, azatonka zai zuba mata idone yana kallonta kamar hoto ko television a gida? ince kwana nan 4 kenan dabaro inda suke”. Wambai yace “amma shine bakiyi maganarba sai yau Granny?”. “to ubana koyamin yanda zanyi”. “ALLAH yabaki hak'uri”. ‘cewar wambai yana k'unk'uni k'asa-k'asa’. Matawalle dabaice uffanba tunda aka fara maganar yay guntun murmushi, muryarsa a tausashe yace, “Ranki ya dad'e ni banga amfanin wannan maganarba, ALLAH shine ya azurta Galadima da samun ciki a jikin matarsa, wannan kuma abun farin cikinmu ne amatsayinmu Na 'yan uwansa, shi dai mulki Na ALLAH ne, shike badawa ga Wanda yaso akuma lokacin da yaso, bamuda tabbacin tsawancin ran ganin gobenmu ma balle maganar gadar sarautar cikinma daba'a San miza a haifaba, please musama zukatanmu sallama kodan mutuwa, nifa banga wani dalili dazamu ke saka kammu a wahala akan mulkin da ubangijine kawai madawwami a mulkinsa, nikam kunga tafiyata, ki gafarceni inada uzuri”. Tunda matawalle yafara maganar Mama Fulani da Talba da wambai ido suka zuba masa, harya fice ba'a samu mai iya tanka masaba. haka yake shi, babu ruwansa da bak'in mugun abun masarautar, da zuciya d'aya yakeson d'an uwansa, shi bama wani zaman k'asar ma yakeba sosai. Wani wawan tsaki Talba yaja, yabi bayan Matawalle da harara yana fad'in “lusari kawai, inkai bakason sarautar mu ai munaso, shifa wannan ko sarautar ya gada wlhy lusarin Sarki mai lasisi za'ayi anan, duk wannan wahalar akansa akeyinta danya zama magajin Abba amma shashashan nan baya gani”. “mtsoww!! bar banza d'an uwa, idan zai bamu matsala kai basai ka zama magajin Abban ba, nifa harma tunani nake, anya matawalle jinin gidannan ne?..........” “kai ya isa haka, banason rashin tauna magana, Ku k'yalesa zaima dawo hanyane, miye mafita yanzun?”. “mafita d'ayace Granny a 6arar da shegen cikin kawai, kuma ma ai Galadiman yazo jiya”. Da sauri mama Fulani ta tashi zaune daga kishin gid'ar datayi, “wambai kana nufin Sameer na a masarautar nan?”. “kwarai ma kuwa, da safe nagansa zaishiga mota a k'ofar sashensa, yanata faman d'aurema mutane wannan shegiyar fuskar tashi da yakejin tafi ta kowa k'yawun gani”. Wani k'asaitaccen murmushi mama Fulani tayi tana fad'in “lallai yaronnan ya isa, kuje kawai, bayan nagama tsara komai zan nemeku”. atare suka mik'e suna fad'in “ahuta lafiya ranki ya dad'e sarauniyar gagara badau”. Murmushi tama jikokin nata tana gyad'a musu kai. ____((____(((★)))____))____ Galadima da Nuren sun shiga ainahin matsakaicin gidan Nuren dake a gidan gonarsa Na kiwo, sosai ya tsara cikin gidan, dan ananne yake holewa da 'yammatansa a watannin baya, sai dai yanzu kam alhmdllh yabari gaskiya, dan sai lokaci-lokaci yake d'an ta6awa, fatansa ma yabari gaba d'aya, dama ta silar abokai ya koya🤦🏻‍♀. Galadima ya zauna saman kujerar guda d'aya yana sauke numfashi, har yanzu zuciyarsa tak'i nutsuwa waje d'aya, halin da yaga Abban Munaya ya dank'are masa zuciya. Cikin ma'aikatan wajen yay sallama daga waje, Nuren yabashi izinin shigowa, kayan marmarine yahad'o ya kawo musu bayan ya tsaftacesu, a saman center table d'in ya ajiye, sannan yakona yaciro musu ruwa a freight d'in dake falon da cups Na glass. Bayan fitarsa Galadima ya kalli Nuren d'in, “Brother wai miyasa ka kawoni nan ne?”. “cinikin kanka nayi”. ‘cewar Nuren yana harar Galadima’. “Wani k'asaitaccen murmushi Galadima ya saki, yakai hannu yana shafa sajensa zuwa gemu, cikin d'age kafad'a da la6e baki yace “baka kai girman saida kainaba yaro”. “uyim! Haka kace ko?”. ‘cewar Nuren yana kallon galadima’. “kaima kasan hakanne ai”. Mik'ewa Nuren yayi yashiga wani d'aki yana dariya, mintuna 4kacal saigashi tare da wani dattijo. Galadima da yake kishingid'e yad'ago ido yana kallon Nuren da dattijon, amma baice komaiba yacigaba da latsa wayarsa hankali kwance. Dattijo direban Alhaji balala ya zube k'asa yana kwasar gaisuwa ga Galadima. Galadima shi mutumne mai mutunta Wanda ya girmesa, dan haka Yakuma d'ago kai yana kallon dattijon, fuskarsa ba'a d'aureba ba'a sakeba, cikin muryarnan tasa ta isar masu mulki da k'asaita yace “no baba zauna da k'yau, kabar durk'usamin banaso”. Dattijo yace, “ai girmanka ne ranka ya dad'e”. Murmushi kawai Galadima yayi, ya ajiye wayar hannunsa yatashi zaune sosai, ruwa ya d'auka ya zuba a cup sannan ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana kallon dattijo. “bawan ALLAH minene sunanka?”. Jikin dattijo Na rawa yace “Barau ranka ya dad'e”. “humyim baba barau, koka sanni?”. “sosaima ranka ya dad'e, wanene zaice bai sankaba a wannan nahiyar”. Galadima ya wani lumshe idanu yana cije lips nashi, ya bud'e idanun akan Mal barau da duk yake a tsure, sosai kwarjinin Galadima da cikar haibarsa suka rikita dukkan tunaninsa da kwarin guywarsa. Galadima ya katse masa tunani da fad'in, “Baba barau nasan akwai tambayoyi taf bakinka a gareni, saidai bazan baka amsar ko guda d'ayaba, zan baka dama da sharad'i, Na farko shine kanada damar fad'amin gaskiyar abinda kasani idan Na tambayeka, nikuma nabarka ka tafi salin alin, Na biyu inada sharad'in ka d'aukarmin alk'awarin komai zai fito abakinka ya zamto gaskiyar abinda Na tambayeka, idan kamin k'arya koka yaudareni kuma.... Humm”. ‘yak'are maganar da cije lips nashi batare da ya k'arasaba’. Hakan yasaka jinin Malam barau rawa, yana karkarwa yace, “insha ALLAHU ranka ya dad'e zaka sameni yanda duk kake buk'ata”. Nuren yace, “good daka fahimci hakan”. Galadima bai sake cewa komaiba yacigaba da latsa wayarsa. Nuren ya kalli Malam barau yace, “malam barau kasan wanene tsohon Sarki?”. “eh kwarai ranka ya dad'e Na sanshi, shine yake jinya a India yanzu haka aiko”. “shin minene alak'ar uban gidanka da tsohon Sarki?”. A rikice Malam barau yace “ranka ya dad'e miyasa zakamin wannan tambayar? Ku gafarceni, kuyi wata amma ba wannanan ba dan ALLAH”. Galadima ya d'ago idanu ya zubama Malam barau su, jiyay zuciyarsa tana Neman fara hasala, har zaiyi maganar sai kuma miya tuna yay shiru ya had'iyeta, maida kansa yayi yacigaba da latsa wayarsa. Nuren ya bud'e k'aramar drowa dake jikin center table d'in falon, saiga bindiga 'Yar k'arama ta bayyana, Malam barau ya waro idanu waje yana kallon yanda Nuren ke d'ura Bullets a cikin bindigar. Galadima duk yana kallon Nuren ta gefen ido amma baice masa uffanba, saida Nuren ya gama sannan ya tashi ya koma kujerar kusada Malam barau, cikin d'aure face yace, “nasan dai tsoron mutuwa ko rasa aiki zai hanaka bamu amsar tambayarmu, to tabbas in baka fad'anba zan fasa kwalwar kanka da wannan gun d'in, kuma ko k'arar fitar bullet d'inta baza'ajiba ballema asan an kasheka, akuma cikin falonnan zan binne gawarka wlhy!!”. Jikin Malam barau Na 6ari yarik'e wandonsa, dan har fitsari yafara fito masa kad'an, yace, “ranka ya dad'e mi kuke son sanine?”. Galadima dake latsa wayarsa hankali kwance, batareda ya d'agoba yace, 20 ga watan Yuli miya faru a masarautar gagara badau”. “ranka ya dad'e wlhy bansan komaiba, amma tabbas ogana yafito ransa a 6ace daga wajen meeting d'in dasukayi da Sarki shida abokansa. daga hakan bansan komaiba wlhy kaji Na rantse maka”. Idanu Galadima ya d'ago ya zubama Malam barau, yace, “malam Saminu kafadda!. koba shine ainahin sunanka ba? Na sanar da kai karkamin k'arya, dan tunkan nakawoka nan nasan komai daya shafeka, amma a tashin farko kamin k'aryar sunanka Malam barau, humm abin dariya, inason mutum mai gardama dason ku6tar da kai. Malam Saminu shiga tarkon Muhammad Sameer ba abune mai sauk'iba, ina aiki da kwakwalwa, kamar yanda gangar jiki take aiki da zuciya, karka yarda a maganarka ta gaba k'arya ta shigo, idan hakan ta kasance saina binneka da ranka, wannan tabbatacciyar maganar Muhammad Sameer Saifuddeen ce”. ‘ya k'are maganar da mik'ewa tsaye yana had'a yatsunsa biyu ya buga a saitin fuskar Malam Saminu, suka bada sautin d'as! d'ass!, sannan ya ra6a ta gefensa yafice’. Nuren ya girgiza kansa, “dattijo kayi kuskure kwarai da gaske, Galadima ya wuce dukkan tunaninka, tashi mu koma inda ka fito, a yanzu kam bazai ta6a saurarenka ba sai kuma wani karon”. Hawaye Malam Saminu yafarayi yana bama Nuren hak'uri, “yalla6ai dan girman ALLAH ka kirashi, wlhy zan fad'a yanzu, wlhy nagaji da zaman kurkukunnan, nasan hankalin iyalaina da mai gidana a tashe take, ka taimakeni”. K'ala Nuren baice masaba, ya dannashi a d'akin ya maida ya kulle sannan yabi bayan Galadima. ★):(★):(★):(★)(★):(★):(★):(★):(★ Tunda suka tafi babu Wanda yay maganar, saida suka shigo cikin gari sosai. Nuren yace, “dattijonnan nakula zaiyi taurin kai gaskiya”. Murmushi Galadima yayi yana kuma lafewa cikin seat, idonsa a lumshe batareda ya bud'eba yace, “mu wuce asibiti”. Amsawa da to kawai Nuren yayi. Sun isa asibiti suka iske duk 'yan gidanmu suna nan, saisu Munubiya da Dady yace su tafi gidajensu hakanan, tundama ba bari ake aga Abban ba basuga amfanin zaman nasuba, gashi mafi yawansu duk da tsohon ciki, sai kuma Munubiya da Fauziyya da Haleematu dake fama da laulayi. Haka ba dan sun soba kowacce takama hanyar gidanta, wadda mijinta kuma yace ta jirasa ta zauna jiransa. Suma su innarmu Yaa Anas ya kwashesu ya maida gida. Lokacin da su Galadima suka shigo asibitin mafi yawansu duk sun wuce, sai mazan kawaine a asibitin. Dan haka Galadima yasamu gaisawa da Munubiya dake jiran yaa marwan yazo d'aukarta. Munubiya ta tambayi 'Yar uwarta fa?, gaban Galadima yafad'i, danshi yama manta su Munaya suna hanya, guntun murmushi yayma Munubiya yace insha ALLAH suna hanya itama, maybe su iso cikin darene kokuma da asuba”. “ALLAH ya kawosu lafiya”. ‘cewar Munubiya tana sharar hawaye’. Tabama Galadima tausayi sosai, haka ya k'arasa wajen doctor domin kumajin ko ansamu wani cigaba a jikin abban.. Doctor yamasa bayanin duk an gyara karayar jikin Abba, hakama sauran ciwukan suna samun kulawa, kuma bugun zuciyarsa ta daidaita bakamar jiya zuwa safiyar yauba. Galadima ya jinjina kai, tareda sake jaddadama doctor gargad'in kulawa da Abba d'in sosai. Yad'an jima a asibitin sannan su sarkin mota sukazo d'aukarsa, Nuren kuma daga nan hotel d'in daya sauka yanufa. ya sauka hotel ne saboda basa buk'atar wani a masarautar su Galadima yasan da Nuren d'in. ___________________________ Wajen misalin 2:30 na dare su Munaya suka sauka, Sauban yayta wayge-wayge ko an zo d'aukarsu, amma baiga alamun wani mai alak'a da masarautaba, ya kalli Munaya yana dariyar tsokana, “Aunty gimbiya Honey d'inki ya manta damu, bai aiko d'aukarmu ba, kuma inatsoron mu shiga motar haya azo a kwamushemu, kinsan yanzun kasuwancin kidnapping shine keda tsada a 9ja”. Duk da Munaya tana tare da damuwa hakan bai hanata yin dariyaba, tace, “kai yaa Sauban bakada dama, ina zamu samu waya mu kirashi to?”. Kafin Sauban yabata amsa sukaji magana a bayansu. “to maganannu, saikuzo mu wuce, wannan surutun nakuma bayasa ayi kidnapping d'in naku ba”. Gaba d'ayansu juyowa sukai suna kallonsa, Galadima ne sanye cikin wando fari 3quarter da riga t-shirt pink mai gajeren hannu. harya kwanta suka fad'o masa a rai, babu shiri yazari mukullan mota yafito, bai tada kowaba a dogaransa saboda kasada irin tasa ya fito zuwa airport, isowarsa baifi da 17minutes ba jirginsu Munaya ya sauka, tunda suka fara fitowa daga jirgin idonsu a kansa, har tsayuwarsu da waige-waigen dasukeyi na son ganin Wanda yazo d'aukarsu yana kallonsu. shagala yay da kallon Munaya, wadda sai a yanzune yaga k'ibar da Samha ke fad'in tayi, ta murje tayi 6ul-6ul da ita, har wani haske yaga ta k'ara masa, saboda hasken daya haske ko'ina a cikin airport d'in. yadad'e tsaye a bayansu, duk gulmarsa da Sauban yayi akan kunnensa ne. Sauban ya k'araso da sauri ya rungume d'an uwansa, dukda jiyane kawai suka rabu saiyaji yayi kewarsa. Galadima yad'an daki bayansa yana fad'in “k'aton banza, ka girma bakasan ka girma ba”. d'agowa Sauban yayi daga jikin Galadima yana dariya, yayinda Munaya da Galadima suka had'a idanu, gira d'aya ya d'aga mata, itakuma tayi guntun murmushi tana kauda idonta gefe. (A ranta tace d'an duniya). Juyawa yayi batare da yak'ara magana ba, Munaya da Sauban sukabi bayansa, Sauban ya shiga baya, badan Munaya tasoba tashiga gaba kusada Galadima da zaiyi driving nasu, wannan ne karon farko da zataga tuk'insa a k'asarsa. Saida yatada motar suka fita daga airport d'in sannan a hankali kamar bataso tace, “yalla6ai mun sameku lafiya?”. Juyowa yayi kad'an ya kalleta ya maida kansa ga titi, saida yaja numfashi sannan yace, “kunzo lafiya my Friend?”. Kallonsa kawai tayi kad'an ta girgiza kai, a zuciyarta tace su Friend anji jiki, zanbika a hakan kodan samun yanda nakeso a kanka, danna cika alk'awarin danama mahaifiyarka insha ALLAH. jin batace komaiba yakuma fad'in “ko gajiyar tafiyarce?”. “kusan haka yalla6ai”. Yace, “to sannu yalla6iya”. Ba Munaya ba har Sauban saida yayi dariya da wannan suna, daganan motar ta d'auki shiru, har suka Isa masarautar. Muftahu dake binsu abaya ya sauke ajiyar zuciya, sannan shima ya shigo masarautar, tunda Galadima ya fito daga sashensa akan idonsane, Dan haka yay saurin bin bayansa da mota shima Dan yaga inda zaije. (Humm Muftahu😏). Sosai Munaya kejin barci da farinciki, yau gata tadawo k'asarta ta haihuwa, sun shiga sashen komai need tagansa, sai k'amshi dake tashi kamar kullum. d'akinta ta shige, Sauban da Galadima suka nufi nasa. Sauban ya zube a kujera yana kiran “wash!”. Galadima ya d'an hararesa, “amma idan yawonkane aibaka gajiya”. “yaya wlhy bazaka ganeba, nidai kawai bani wajen kwana na kwanta wlhy”. “Saidai ka kwana anan falo kuwa, kafin da safe a gyara sashenku ka koma can”. 6ata fuska Sauban yayi, “haba Yaya da gatana na kwana saman kujera, kadai katafi d'akin Aunty gimbiya ka kwana gaskiya kabani gadonka”. Galadima zaiyi magana Sauban yatashi da gudu ya shige bedroom d'insa ya saka key. Da sauri Galadima yace, “zan 6ata maka rai fa Sauban”. Ina, baima sauraresa ba, dafe kai Galadima yayi kawai, wlhy baisan lokacin da Sauban yafara rainashiba, kodan yaga tsawonsu kusan d'aya yanzu?. babu yanda ya iya dole yafita zuwa d'akin Munaya🤫.................✍🏼 Ho Sauban aikinka yay k'yau🤣, su Galadima dole a tafi😝, ba ruwana karya jini🤭⛹🏻‍♀ Readers kuma kuyi dariya a hankali fa🤫😝. Barkanku da juma'a🙋🏻. Musha weekend lafiya sisters😁🙋🏻⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu😭🤚🏻✋🏻_* AWESOME WRITER'S ASSO..🏮 (palace of excitation and pleasant writer's) INA TARE DA ITA! 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾 (bansan ita bace) 🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾🐾 Story & written by mmn fareesa Wannan page din nakune INA TARE DA ITA fans club gsky naji dadi sosai da comments dinku na jiya dan yafi na kowa😻😻 NOT EDITED 🅿69&70 Kafin tayi mgn taga get man yabudewa yah Suleiman get ya cinno hancin motarsa ....wani irin bugawa kirjinta yyi sbd tunawa datayi da warning d'in da yah Suleiman yyi mata game da maganar Abbas din agabanshi... Shikuwa Abbas kallon ta yake yanata zuba surutunsa har yalura tana duniyar tunani"fuskarsa ya matsa gab da tata yahura mata iskar bakinsa....adede nan Yah Suleiman dakeyin parking idanunsa suka hasko masa baby da wani gab da juna dan saiyaga kamar kissing d'in ta zaiyi.. Wani mugun burki yaja,yana huci yafito azafafe ko murfin motar be rufeba yanufi gunsu. Wani irin zafi da k'una yakeji azuciyar sa afili yace gsky yarinyar nan ta rainani ,amma zanyi maganinta dg shi har ita,yafad'a idanunsa sunyi jajir zuciyarsa nace masa ko shine ABBAS?" Azafafe yakoma mota yaciro bindigarsa yanufo gunsu... Baby kuwa tunda ta ga yadoso gurunsu atsorace ta kalli Abbas daketa tambayar ta tunanin me take haka?" Murya na rawa sbd tsoro tace pls yah Abbas kabar gidan nan yanxun ga yah Suleiman nan kuma wlh zai iya maka illa dan zafin zuciya ne da shi" D'agowa Abbas yyi yahango jarimi ,sadauki ingarman namiji cikin kakinsa na sodoji. yanufosu sai kuma yaga yajuya gun motarsa. Da sauri yace wanene shi ?"meye matsayinsa agunki? da kika tsorata dan yaganmu tare da ke matsayina na Wanda zaki aura.....maganar ta mak'alemasa ganin yah Suleiman din yasake nufosu da bindiga ahannunsa. Salati baby tayi sai hawaye shar afuskarta ta San lallai yau me kwatar Abbas gunsa sai ALLAH . Shikuwa yah Suleiman wani mugun kallo yake jifarsu da shi yana ganin duk Dan sbd Abbas din ko waye take zubda hawayenta sbd shi bata sonsa aidama be manceba tace bata sonsa Abbas take so. Kamar yadda shima baya sonta IFTI ce aransa...tuni yasake zuciya bbu annuri a fuskarsa ya ida isa gunsu.. Abbas kuwa daurewa kawai yake amma hankalinsa inyyi dubu tashe yake sbd yalura bbu sassauci afuskar yah Suleiman din ." Cikin tsawa had'e da karaji yace kai dan k'auye !dak'iki me yashigo dakai gidan mutane?"bbu izininsu.....da sauri baby ta katsesa da pls yaya kayi hkuri wlh na laifinsa bane laifinane amma yah Abbas be.....wani gigitaccen mari yawanko mata "saida taga stars namata shawagi tuni tadafe gurin tasaki k'ara.. Abbas yyi karfin halin cewa gsky wannan ba adalci bne dazaka kamata kadaketa sbd..wata wawar fincika yah Suleiman yyi masa had'e da makasa jikin bango atake bakinsa yafashe. Cikin isa yah Suleiman yace yes na mareta sbd na isa ne kuma kaima yanxun zan Nuna maka isata ta hanyar yimaka hukunci da laifinka duk da nasan.bakasan wanene niba! Tuni yasaita bindigarsa zai harbi Abbas ....da sauri baby dke tsaye dafe da kunci tana kuka tamatsa gaban Abbas cikin dakiya tace ah ah ni zaka kashe bashiba ,ta fad'a had'e da tare Abbas d'in kafin yah Suleiman yyi wani abu yaji Abba abdullahi na masa tsawa had'e da cewa kada kasake kayi Harbin nan....tuni yah Suleiman yyi wurgi da bindigar ya finciko baby da hannu daya ,hannudaya yakaiwa abbas wani wawan punch a fuska tuni hancinsa yafashe yyinda Abba ya iso afusace ya wanke yah Suleiman da mari had'e da cewa me yamaka ?" Beyi mgn ba idanunsa sunyi jajir jijiyoyin kansa duk sun mik'e rad'o rad'o, yanajin zafin hanasa da Abba yyi yama Abbas hukunci......sai botsare botsare take tanaso yacikata ta taimakawa Abbas ganin halin dayake kuma sbd ita"amma yarik'e ta gam. "Abba ne daya lura yah Suleiman bazaiyi bayaniba sbd dokin zuciyar dayahau " yasa Yakama Abbas suka nufi get . Shikuwa gogan ganin abinda baby keyi yasake bata masa rai azafafe yadauketa da bindigarsa yyi part d'in sa da ita tanata ihu da kiran sunan Abbas din. Abba kuwa suna fita saiga motar yah Yusuf tuni yatsayar dashi suka shige hade da nufar asibiti. Bayan duk anbasa treatment d'in da yadace aka samasa drip had'e da yimasa allurar bacci sannan Abba yakira abbu yace su had'u a asibitin. Shikuwa yah Yusuf yanufo gd yana tambayar kansa wanene wancan saurayin ?"kuma waye yajimasa ciwo haka acikin gidan?" "Xuciyarsa tace yah Suleiman ne" Shiru yyi had'e da yin parking yafito yanufi part d'in su...zubaida dke kallonsa ta window tana Dakon zuwansa tun dazun ,jitake kamar ta bisa saidai zuciyarta nace mata hmmm kije kici dukaba.... ********** Abbu kuwa byn yaje asibitin nan Abba yyimasa bayanin iya abinda yasani game da abbas,ajiyar zuciya yyi yace hmmmm wannan Yaro ALLAH yarabasa da Wannan zafin zuciya tasa! Yanxun dabakazoba fazai iya kissan kai "oh ALLAH yakyauta ,amma yanxun mujira asallamesa muwuce gd naga Suleiman din yyimun bayani meye hujjarsa na zubarwa da wannan Yaro jini. Abbu yyi ajiyar zuciya afili yace gsky yaya Wannan karon zan yadda kwallon mangwaro na huta da kuda.. Abbu da mamaki yace mekake nufi?" Abba yyi masa bayanin abinda yafaru da mm zulai dg karshe yace datadawo takardar sakinta zanbata nagaji wlh bazan iyaba ,mace daya nasan samun hawan jini da bacin ciwon zuciyar data samun... Cikin rarrashi da ban baki abbu yace ah ah bazaa yi hakaba kodan sbd y'ayanta,kak'ara hkuri dan ALLAH kaje kabiyasu ayo Belin nata....katsesa yyi da cewa ah ah wlh kokai ban amince ka biyaba gwara abarta can kotasaduda da duniya.... Kiran sallar laasarne yasa suka fita masallacin , kafin sudawo ya farka ancire masa drip,bbu laifi jikin yyi masa sauki saidai yasha alwashin bazai koma gidan su baby ba yanxun zai koma kauye ko da dare ne ya isa"sbd yatsorata da sojan nan dan yatabbar mutumin bashida imani,inbachin yanada sauran shan ruwa da sai dai wani bashiba ,saidai yasha alwashin daya sauka gd zaije gun mlm yyimasa bayani ,wanene sojan nan?"meye matsayinsa agun nah nah? """"" Saurin tashi yyi ganin bbu kowa a room d'in dan beso ma su had'e da Abba daya taimakesa yakasa asibitin, yyi saurin ficewa yyi tasha yahau motar garinsu... Su abbu nadawowa suka sami room d'in wayam,bbu Abbas bbu alamarsa ,nan suka tambaya a reception akace ai ya fita ,abbu yacewa Abba to shikenan ALLAH shi kyauta muje yanxun gd ni naga Suleiman din dolensa yyimun bayani da haka suka nufi gd... ----------------------------------- Bangaren mm zulai kuwa tun amota take hawaye tana gayawa Laure saita d'au fansar abinda Tamara,dariya Laure tayi tace hmmm wlh zakijawa kanki natona abinda kika binne....cikin ko inkula mm zulai ta ce eh ai harda ke ,baki daya zaki tonama asirin .....police guda yace malamai kuyimana shiru,tsit sukayi harsuka iso aka saka mm zulai cell,aciki tasami wasu mata 8itace ta Tara ta tsorata ain in dan bata taba zuwa police station ba sai yau jiki bbu kwari ta zauna aka rufesu ciki. Sai kallon su take tana Dade hanci sbd wari da zauri da gurin keyi,tuni tafara jin tukar amai sbd ko break batayiba aka taho da ita. Kakarin amai ta fara ...cikin matan dake cell din wata tantiriya y'ar tasha ta watsawa mama zulai mugun kallo had'e da cewa ke karamar y'ar iska! Zakixo Okinawa mutane iyayi d hura hanci ke mai tsabta harda yunkurin amai ko?in har da gske ke me tsabtar zuciya ce bazakiyi laifi akaiki police station....afusace mama zulai tace ke matsiyaciya karamar y'ar bariki me ruwanki dani dazakizo kinamun halin dabbanci... Azafafe tayi gun mm zulai had'e da mata wawar fincika tacigaba da jibga ,tun mm zulai na iya ramawa harta tagayyara sbd batayi break ba,tuni matar ta kumbura mata fuska ,sukuwa sauran dama tsoron matar suke basuce komai ba harta gaji ta kyale mm zulai din ta yi kwance yashe kamar kayan wanki. Zuwa 12:00 har jikinta yyi zafida zazzabi da ciwon kai, mace daya ce mai dan tausayi tasanar da Wanda yakekae musu abinci ,yaje yakarbo magani yakawo ,byn taci abincin da ko almajiri bazata iya bashiba tasha maganin ,tana tuna yayanta da gd tana hawaye... Yah Suleiman kuwa.. Share.. 📚📚mmn fareesa ce✍✍ *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻6⃣ ............Har ya fita ya dawo, laptop da wasu takardu ya d'auka a falonsa ya fita, zai zauna a falonta saikuma wata dabara ta fad'o masa, bedroom d'inta ya nufa yana wani ciccijewa (kaida zaka karoro, miye na fuska to yalla6ai?🤔😂). Munaya Na tsaye tana ninke hijjab d'in data rama sallolin dasuka risketa a hanya sai kawai shigowarsa tagani da sallama ciki-ciki. k'ok'arin warware hijjabin tafarayi tana masifa ita kad'ai a zuciya, haka kawai aita shigoma mutum d'aki babu izini, wannan wane irin rayuwane. Shikam Galadima kallo d'aya yamata ya d'auke kansa, Dan daga ita sai zani d'aurin k'irji. Laptop d'in hannunsa da takardu ya ajiye a bakin gadon, sannan shima ya zauna, batare da ya kuma kalllon Munaya ba yace, “kinajin yunwa ne?”. Ba yunwar takeji ba, amma dan Neman magana kawai tace “eh”. Kallonta ya sakeyi, bata yarda sun had'a idoba, yace “Saidai kisha fresh milk kuwa, dan bani da abinci”. Manyan idanunta ta waro masa waje, kamar wadda akace tasha wuta, cikin dafe k'irji tace “yalla6ai fresh milk?”. Da mamaki ya kalleta, danshi bai fahimci ma'anar razanar tataba, yace, “uhmmm”.... “Na yafe wlhy”. Tafad'a da saurinta. “To mine nawani birkicewa haka? fresh milk d'in wani abune dashi?”. “Humm”. Munaya tafad'a tana ta6e baki, tace “yalla6ai nikam idan kaga nasha fresh milk d'in data fito daga d'akinka saidai idan bana a hayyacina”. Da tsantsar mamakin furucinta yake kallonta, da yake basuda nisa saiya mik'a hannu ya rik'o nata, zatayi magana ya fizgota ta zauna kusadashi, kad'an ya rage ta hau masa laptop, amma yay saurin janyewa da d'ayan hannunsa. “wash hannuna”. Munaya tafad'a tana matse baki. Banza yamata, yakuma matsa hannun da mugunta. tasaki k'aramar k'ara tana fad'awa gefen kafad'arsa. Ya d'an kalleta ya janye yana ta6e baki “ban fahimci zancenki daga nesa ba, maimaitamin”.. Cikin tunzuro masa baki tace, “yoni babu abinda nake nufi fa, nidai bazan sha fresh milk d'in data fito daga d'akinka ba wlhy. haka kawai aje asakama mutum abinda zai halakashi”. ‘k'asa-k'asa ta k'arasa maganar, amma yajita sarai’. Shifa saima yanzu yagane inda zancenta ya nufa, wani miskilin murmushi yasaki yana danne dariyarsa datake shirin kufcewa, amma dukda haka saida taji sautin fitar murmushin nasa. Munaya dake satar kallonsa idonta harya cika da kwalla, a zuciyarta tace mugu d'an masa, dole fa kamin dariya. Saida yayi dariyarsa a zuciya ya gama ya kalleta, itakuma saiwani mar-mar takeyi da idanu wai zatayi kuka. Murmushi ya kumayi, sannan yace, “wannan bakin dakike tunzuromin ko, hummm.....”. ‘yak'are maganar da cije lips nashi’. Yunk'urawa tayi zata mik'e, tace, “yalla6ai ni wlhy barci nakeji fa”. Dawo da ita yayi ta fad'o jikinsa shima yana fad'in “nikuma gadinki zanyi ko? yalla6iya!”. Tace “wayyo innarmu kice ya fitarmin a d'aki please”. “ko waya zan baki ki kiratane”. ‘yay maganar cikin d'age gira d'aya’. Munaya tai saurin janye idanunta daga Kansa ga k'amshin turarensa ya gallabeta, barci takeji, amma takula mugunnan soyake ya hanata ma. Kamar zatayi kuka tace, “yalla6ai wai mikazo nemane please? Wlhy barci na keson yi?”. Shiru yamata, saida ya mula dan kansa sannan yace “jikina fa”. ‘yay maganar yana kallon k'ugunta’. Da sauri Munaya ta sauka daga jikinsa tana k'unk'uni da tura baki. Medical glasses d'insa ya d'auka ya saka, tareda cigaba da aikinsa a laptop, a zuciyarsa yana fad'in yarinyarnan akwai ruwan tsiwa, amma duk randa Na kama bakin tsiwarcan sai yamin bayani dalla-dalla kuwa. Ganin ya shareni ya cigaba da sabgarsa a System, nima sai ban kuma bi ta kansa ba Na d'auki kayan barcina nashiga bayi domin Na sanya. Sai dai zuciyata cike take da fargabar miya kawoshi d'akina?. haka na fito kamar wata munafuka ina lallak'ewa jikin bango. Duk yana kallona ta gefen idanu, amma yay kamar baima San dani a d'akinba. Sai zuwa can ya d'ago yana kallona, yana wasa da pen d'in hannunsa kan la66ansa, “idan bak'yajin barci zokimin wani d'an aiki nan”. Saida gabana ya fad'i, a raina nace aikin mi kuma?, a fili saina aro jarumta na yafama kaina, Dan nakula tsoron daya fara gani a idona ne yake neman fara rainani da samin fargaba (🤣ho munayan shagali). Takowa nayi inda yake, ina niyar zama bakin gadon sai ya nunamin tsakiyar gadon, shima laptop d'in ya tura sosai kan gadon ya haye tsakkiya yana gyara zamansa. kuma had'e fuska nayi ina wani dojewa na hau nima na zauna, cigaba yayi da danna laptop d'in, kusan mintuna 3 ya jehomin tambaya. “shin kinsan minene aikin Abba?”. Da mamaki na kallesa, nace “wai Abbana kake magana?”. “uhmm”. ‘yafad'a batare da ya d'agoba’. Shiru nayi alamar tunani, harya d'ago ya kalleni bance komaiba, maida kansa yayi ga laptop d'in yacigaba da aikinsa, zuwa can nace, “ma'aikacin gwamnati ne kawai tawani fanin kuma aikinsa yanada Nasaba da jarida”. Tunda nafara magana ya tsuramin idanu, bakina kawai yake kallo yana taune lips nashi, saida nakai aya sannan yace, “jarida?”. Nace, “eh, wani abune ya faru?”. Kansa ya girgizamin, “innalillahi” yashiga maimaitawa a zuciyarsa, baya fatan zarginsa yazama gaskiya, cikin dakiya yakuma cemin “kokin san abokansa? ina nufin cikin manyan mutane haka?”. “eh to, akwai senator halluru garba, sai kuma wani anacemasa Alhaji Mamman k'afur, last year yafito takarar shugaban k'asa......” Caraf ya kama hannuna, “kina nufin Alhaji Mamman k'afur abokin Abban kune?”. Ni tsoroma yabani, yanda yay maganar cikin rawar jiki, na jinjina masa kaina a hankali. Gani nai ya taune lips nashi da masifar k'arfi, ya kaima iska naushi. da sauri na matsa baya Dan karya nausheni, ganin kamar na tsorata sai yay murmushi, cikin k'asaitacciyar muryar nan tasa yace “my Friend! Yanzu ne zamu fara aiki tare da gaske ni da ke”. “kamar ya yalla6ai? wane irin aiki kuma?”. Murmushin takaici yayi, ya kalleni ido cikin ido, kasa jurewa nayi nai k'asa da nawa. shima lumshe nasa yayi yana fad'in “zaki gani”. daga haka ya janye laptop d'in gefe ya zame ya kwanta. Binsa nayi da kallo tamkar wata sokuwa, gaba d'aya ya kulle magudanar tunanina da wadda ke kaima kwakwalwata sakonni. Medical glasses d'in idonsa ya cire ya ajiye, sai kuma ya juyo gareni, hannunsa d'aya ya mik'amin yanamin alamar nazo gareshi. Idanu na d'an zaro, sai kuma na nok'e kafad'a alamar nak'i din. Wani murmushin da bako yaushe yakeyinsaba ya sakarmin, ya juyamin baya yay kwanciyarsa. bai sake juyowa gareniba har kusan 6minutes. nagaji da kallonsa da nazarin murmushinsa da tambayoyinsa na janye idanuna, waishi guy d'innan mike damunsa ne? gaba d'aya ya canjamin daga saukarmu zuwa yanzun, dubana nakai ga agogon d'akin. 3:27am, “ya salam” na fad'a a hankali, muna Neman kwana a zaune. can k'arshen gadon na koma na kwanta, zuciyata cike da tsoron ALLAH yasa bawani Abu ya shiryaminba, babu dad'ewa barci 6arawo ya saceni. Numfashina dake sauka a hankali yasaka Galadima gane nayi barci, juyowa yay yana kallona, yayinda zuciyarsa keta cud'a amsoshin dana basa yanzun, tabbas mahaifin yarinyarnan akwai abinda yasani, kwarai da gaske zaiyi amfani da ita wajen gano ko wanene mahaifinta?, minene alak'arsa da case d'ina?, sannan minene alak'ar Muftahu da ita?, Dan tabbas akwai manufar sako yarinyar acikin wannan tak'addamar, kuma Muftahu dashi aka shirya komai. yasaki wani murmushin mugunta tareda nuna kansa, a fili yace _MAK'IYAN MAHAIFINA SAINA ZAME MUKU_ *RAINA KAMA KAGA GAYYA* tabbas lokaci yayi dazakuga wannan *Gayyar*. Tofa masu karatu, ana zaton wuta a mak'era🤔, mikuna yasako Abban munaya a rikicin masarauta? Kodai ba masarautar kawai bace keda alhakin ciwon tsohon Sarki Saifudden Abubakar🤔?, shin tsakanin Galadima da Munaya & munubiya, innarsu Munaya. Wanene RAINA KAMA...... d'in🤗?. Kumuje zuwa kudai my Guy's😁, duk nisan jifa👆🏻, k'asa zai fad'o👇🏻🤗 ★___________________________★ Bayan shigewar su Galadima Muftahu ya fito daga mota shima yana murmushin dashi kad'aine yasan fassararsa, jiyay kawai handkerchief ya rufe masa fuska, yay saurin cirewa yana waige-waige dan dunba wanene ya jeho masa, wayam babu alamar mutum a wajen, bai gama dube-duben ba yay luuu zai fad'i, saigashi a hannun mutum, idanunsa sunriga sunyi nauyi, dishi-dishi yake kallon Wanda ya tareshi d'in, dama gashi ya rufe rabin fuskarsa ba'a gani, wasu samarine su biyu sukazo suka kama Muftahu tareda wancan suka danna a mota, tun yanajinsu sama-sama har idonsa da jinsa suka rufe baki d'aya. 🙆🏻tofa suwaye?. ★__________★_________★ Tun kusan around 8pm Nuren yake k'ofar wajen, a dukkan bayanan daya samu daga majiya mai k'arfi yarinyar Minister ta shigo gari yau, kuma zatazo shan ice-cream wajen, wayarsa ya d'auka yay wasu 'yan danne-danne, murmushi yayi ya maida wayar ya ajiye tareda dasama k'ofar wajen idanu, dolene kafin tashiga ciki zai saceta, dan bincikrnsa ya nuna masa cctv camera d'aya ce a cikin wajen kawai, a waje babu, dan haka bama ya buk'atar ta Shiga, murmushi yayi saboda ganin motar da driver d'inta yamasa kwatancen zasuzo aciki, saida driver n yaga motar Nuren sannan yazo kusada ita yay parking, bud'e murfin gefen mai zaman banza Nuren yayi, hakan kuma yay dai-dai da fitowar zankad'ed'iyar budurwa daga motar datai parking kusada ta Nuren d'in, murfin ne ya daki gefen hannunta kad'an. A fusace ta kalli motar Nuren, shikuma yay mata murmushi, wani haushine ya kamata, banda rainin wayo ya bigeta amma yamata murmushi saboda wulak'anci, yau saitaga wanene ubansa a garinnan?. da k'arfi tabuga saman motar tana lek'a kanta ciki, “kai wawa bakaga abinda kayi bane?”. Maimakon ya bata amsa saiya jefa mata handkerchief d'insa saman fuskarta, janyewa tayi da sauri zatayi magana kanta ya sara mata, da lalube ta dafa kujerar motar ta shiga ta zauna, sai faman lumshe idanu takeyi. murmushi Nuren yayi, ya taimaka mata ta ida shigowa Sannan ya rufe motar, komai akan idon driver n ta ya faru, bashida damar hanawa, dan Nuren yasashi a tsaka mai wuyane. Agaban idonsa Nuren yaja motarsa yabar wajen yana murmushin samun nasarar tafiyar plan d'insa yanda ya tsara. a wannan daren yanufi gidan Galadima dake can bayan gari inda aka ta6a kai Munaya. 😱humm yau 'yar kidnapping akeyi kawai😂🤪. ------------(((★)))-------------- Galadima yariga Munaya farkawa, dama bawani isashshen barci yayiba, tunani da damuwa suka taru suka hana idonsa rintsawa sai gabannin Asuba. Ana kiran sallar farko kuma yana farkawa, tashi yay zaune dafe da kansa, kusan mintuna biyu ya juya yana kallon munaya data juyo tana fuskantar inda yake yanzun, da gani kasan barcin bamai dad'i takeyiba, dan sai yamutse fuska takeyi a cikin barci. matsawa yayi kad'an ya d'ora yatsunsa biyu gefen fuskarta, sai yaji zafi jikinta, ya janye yana mamakin wai mike damun yarinyar nan kwana biyu haka? dolene yau yasata taga doctor idan sunje ganin Abba. gabansa yad'an fad'i daya tuna har yanzu itafa batasan komai ba, shi baima San ta yadda zai sanar mata abbanta yana cikin mawuyacin hali ba, ya dafe kansa yana ambatar sunayen ALLAH kozaiji sassauci a ransa. Da k'yar ya samu ya mik'e domin yin rakata ainul'fijir kafin akira assalatu. Bayan ya idar ya tadani, da k'yar na iya tashi dafe da kai, dan barcin bai isheniba, muryarsa da alamun shima rashin isashshen barcin yace, “time d'in salla yayi”. Idona dake bud'ewa da lumshewa Na kad'a masa alamar amsawa, yay saurin janye nasa saboda wata fad'uwar gaba da tsirgawar wani Abu dayaji lokaci guda tun daga Kansa zuwa yatsan k'afarsa, bai sake magana ba yafice. nikuma nakoma Na sake kwanciyata. 'Dakinsa ya shiga ya tada Sauban dansu tafi massalaci. Babu dad'ewa Sauban ya kammala alwala yafito ya iskeshi a falo yana jiransa, harara ya antayama Sauban, shikuma ya kauda kai gefe yana had'iye dariya (yo daga taimako saiya zama laifi?). Sarki yayi mamakin ganin Sauban, dan yaron bawani zuwa k'asar yakeba saida dalili mai k'arfi, bayan yagama k'ar6ar gaisuwa wajen jama'arsa Galadima da Sauban sukabishi zuwa sashensa. Kasa 6oye mamakinsa yayi, ya kamo hannun Sauban d'in dake d'ayan 6arinsa zaune kamar yanda Galadima yake, “yarona ne yau ak'asarsa ba biki ba ba bikin salla ba?”. Dariya Sauban yayi, yace “Abba nazo gaidakune kawai”. Sarki ya Murmusa yana kallon Galadima, “Galadima kodai akwai abinda ke faruwane kuke 6oyemin?”. Galadima ya d'ago kansa cikin damuwa yace “babu abinda muke 6oyewa ranka ya dad'e. Mahaifin Munaaya ne yay Accident shine suka taho da Sauban d'in”. “mu bamuda muhimmancin da zamu Sani kenan ko?”. “ALLAH ya huci zuciyarka ba haka nake nufiba, bayan barina wajenka jiya nima aka sanarmin, lokacin dana shigo kuma dare yayi”. Ajiyar zuciya mai martaba ya sauke, yace “ALLAH yabashi lafiya, zuwa anjima sai su waziri suje dubashi ai, tana ina ne ita d'iyar tawa?”. “tana nan cikin masarauta”. Jin jina kai kawai Sarki yay bai kuma cewa komaiba, sai zuwa can yacigaba dayima Sauban tanbaya akan jikin Abie, shikuma yana bashi amsa. Galadima dai Na jinsu bai saka bakiba. ************* Saida gari yafara haske ALLAH yabani ikon tashi, dan zazza6in kuma ya sauka, yanzu kuma haka yakemin, da dare yayi zan fara zazza6i, lokacin da gari zai waye saikiji ya sauka. Sai dai ciwon jiki. Saida nayi wanka da ruwa mai zafi sannan nayo alwala, sallar asubahi data kwacemin nayi, Na jawo handbag d'ina danazo da ita Na d'akko wayata, sim card d'ina Na 9ja Na d'akko shima Na saka akan wayar, massage suka turomin Na adadin awannin da suka bani sim card d'in zai d'auka kafin ya cigaba da aiki. ganin haka saina ajiye wayar natashi domin gyara d'akin, ina cikin kakka6e gado idona yakai bisa wayar Galadima. dad'ine ya kamani, koba komai nakira wani d'an gidanmu Na sanar dasu nazo 9ja. Wayar Na d'auka Na saka number Abbana, dan yanzu nafi kwad'aituwa dajin muryarsa fiye da kowa, kodan mafarkai marasa dad'i danakeyi a kansa, Mtn d'insa nafara kira amma a kashe, saina kira glo d'in, shima switch up, ban kawo komai a rainaba na maida kiran kan innarmu, bugu biyu aka d'aga, wani dad'ine ya kamani, cikeda d'oki nace “innarmu I miss you”. Aiyaan daya d'aga wayar yay dariya, aunty ba inna baceba. Nine, Nima Na iya waya yanzun”. Dukda naji dad'in jin muryar d'an uwana, hakan bai hana zuciyata shiga fargaba ba, nace “Aiyaan Kaine? ina innarmu d'in?”. “Tana wanka ne zamuje asibiti wajen Abba”. Da sauri Na dafe k'irji, nace “Asibiti kuma? miya sami Abban?”. “Lah Aunty baki saniba? Ai accident yayi fa, kuma innarmu nata kuka, hakama innaro dasu daddy”. “Aiyaan!!...” nafad'a da k'arfi, kafin nace wani Abu naji an rik'emin hannu ta bayana an zare wayar daga kunnena. Kuma rikicewa nayi, Na juyo da hanzari, cikin kuka naketa fad'in “abbana! Abba da gaske Aiyaan yake yi? Yalla6ai da gaske Abbana yayi accident?”. Wani tausayina yaji ya tsargashi, ya dafa kafad'una, cikin sigar lallashi yace “cool down mana my friend”. “to ka fad'amin da gaskene Abbana yayi accident d'in?”. Rasa mizaice min yayi, sai bin fusakata da idanu yakeyi, ya cije lips nashi yana fad'in “inhar kinason na kaiki ki gansa toki nutsu”. Share hawayena nayi da sauri nace, “to na nutsu muje”. Yaja hancina, a hankali ya furta, “good girl”. Sai ya juya kuma ya fita. Binsa nayi da kallo hawaye na zuba a kumatuna, kenan da gaske Aiyaan yakeyi Abba yayi Accident d'in, “hasbinallahu wa'ni'imal wakil”. Na dafe kaina tareda zama a bakin gadon nacigaba da raira kukana. Shikam yana fita ya dunk'ule hannunsa yana cije lips, yama akayi yabar wayarsa harta d'auka tayi kira dashi, ko kad'an baiso hakaba. Baiso tajiba kai tsaye. Saida naci kukana na gode ALLAH sannan natashi na hau shiryawa, atamfa na saka zani da riga, bawata kwalliya nayi ba, na shafa fauda kawai da lips gloss, turarema kad'an na shafa. ina cikin Neman mayafi ya shigo, kamshin turarensa yasani juyowa na kallesa, sanye yake cikin oxblood d'in shadda, hularsa takalmi agogo duk black, link d'in hannun rigarsa yake sakawa, sai alk'yabba pink da ratsin milk a hannunsa. d'auke kaina nayi naci gaba da neman gyalena a cikin kayan lefena. Baimin magana ba ya tako har inda nake, hannu yasaka a kafad'una ya d'agoni, fuskarsa babu walwala ko kad'an, idonsa akan fuskata, kusancin damukai da juna sosai yasaka numfashinsa ke sauka akan fuskar tawa, janye idona nayi na maida kan design d'in gaban rigarsa, yayinda shikuma ya warware alk'yabbar hannunsa mai k'yau ya sakamin, d'agowa nai muka k'ara had'a idanu, ya jinjina min kansa kawai. Jinai tamkar in fasa ihu, banason saka alk'yabba d'in nan nidai, dan nauyi sukemin, garama wannan batada nauyi gaskiya, dan tamkar riga After dress take, saidai suffar alk'yabba aka mata, kuma tanada kaurin dabaza'a ga jikin mutumba. Hannunsa yakuma d'orawa akan kafad'una ya d'ago hular alk'yabbar dake kwance a baya ya sakamin, ni kaina koba'a fad'aba nasan nayi k'yau, yanzunma baice uffanba ya juya ya fita yana nunamin agogon hannunsa alamar time yana tafiya. Handbag d'ita na d'auka da wayata nabi bayansa, dauriya kawai nakeyi na hana kuka tasirin zubowa. A falo na iskeshi shida Sauban dake zaune a kujera shima cikin manyan kaya, dayake ba sakawa yakeba sainaga ya canjamin, ya kalleni cikin halinsa na tsokana yana fad'in “kaga sarauniya gagara badau ta gobe, takawarki lafiya 6auna mai tafiyar k'asaita.......”. Harar da Galadima ya zuba masa ce ta sakashi gimtse bakinsa yana had'iye dariya. Nidai banma tankaba, dan yau zuciyata babu dad'i. Galadima ne yay gaba mukabi bayansa, tunda muka fito hadimansa suke zubewa gaishemu, Sauban kawai ke amsa musu, shikam Galadima saidai d'aga hannu, Niko ko kallonsuma banayi. Hakan yasa suka fahimci har yanzu akwai matsala kenan, dansu bama Susan munzo nida Sauban ba. Muna k'ok'arin shiga mota Harun ya iso wajen, gaidashi Sauban yayi, nima na gaidashi, ganin ni da Galadima kowa fuska a tamke sai abin yabashi mamaki, hannun Galadima ya kama suka koma gefe. Nikuma da Sauban muka shiga mota. “Sameer babu fad'a miya kawo gaba?”. Murmushi Galadima yayi, ya cije lips nashi kad'an yana kallon Harun, “bazaka ganeba Harun, na iske abinda ya dagula lissafinane kawai, naga kiranka jiya, amma ina cikin rud'ani a time d'in shiyyasa ban d'agaba”. “rud'ani? mike faruwa ne?”. “mahaifin munaya ne yay Accident, a time d'in ina hospital wajensa”. “ya salam, ya jikin nasa to?”. “Alhmdllh, zamuje canne bayan mun gaida jama'ar gidan”. “ok bara na k'arasa abinda zanyi kafin Ku fito saimuje”. Kai kawai Galadima ya jinjina masa. Bud'e masa gefena akayi ya shigo, yad'an kalleni, kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru. Sashen mama Fulani muka fara Isa, amma sai aka sanar mana tasha maganin mura ta kwanta, daga nan muka nufi sashen matan Sarki, inda yafi ko ina k'awa da ado a gidan kenan. Mun sami tarba ta musamman ga Uwar gidansa, nidai matarnan tana k'aunata na lura, kuma tafi sakarma Galadima fiye da kowa a Matan sarki, tanada kirki sosai, haka taita jan Sauban a jikinta, nakula suma sunfi sakewa da ita. Sosai ta nuna damuwarta akan Accident d'in mahaifina da Galadima ya sanar mata, taita jinjina maganar tana lallashina da jerama Abba addu'ar tashi cikin k'oshin lafiya. Tasa aka kawo mana break fast wai saimun karya anan, Sauban ne kawai yaci, amma Galadima cewa yay ya k'oshi, nima nace bazan iya ciba. dan burina kawai naga mahaifina, gaisuwarma duk akan k'aya nake. Shima Sauban d'in bai wani ci abun kirkiba yace ya k'oshi, mun fito muka shiga sauran sassan, amma ba ko inaba. Sauban da harun sun tafi a mota d'aya, nikuma ni da Galadima. Sai motar dogaran Galadima guda biyu, sai kuma kuyangi hud'u da Uwargidan sarki gimbiya Zulfah tahad'oni dasu, wai kafin mu dawo nima a turamin bayina da zasu ke kula dani, ni dai da to kawai na amsa, Galadima kam baima ce uffanba. Babu mai magana a cikinmu daga ni harshi, sai saukar ajiyar zuciyata da share kwalla time to time danakeyi. ............................................ Innarmu na fitowa daga bayi Aiyaan ya sanar mata na kira, da mamaki tace masa kodai Munubiya ce?”. “wlhy Innarmu aunty Munaya ce, kuma batasan Abba bashida lafiya ba”. “ka sanar mata ne?”. tafad'a a rikice. “eh innarmu na sanar mata, kumafa naji tana kuka”. “innalillahi Aiyaan wayace ka sanar mata? da wace Number ta kira?”. Tayi maganar tamkar zata make Aiyaan. Runtse idanu yayi yana k'ank'ame jiki saboda tsoro. innarmu dukta rikice, tasan su Munaya da shiga Rud'ani akan Abu, yanzu haka tana cikin damuwar Munubiya itama, dan jikinta yakuma janga6ewa, ga laulayi ga wannan damuwar Abban. K'ok'arin kiran Number tashigayi danta kwantarmin da hankaki amma sai tak'i shiga. Har suka gama shirin asibiti wayar bata shigaba. Koda suna mota taita gwadawa. A asibitin suka had'u da mama Rabi'a suma sunje, ganin innarmu a cikin damuwa yasata k'ok'arin fara kwantarma 'Yar uwarta da hankali. Innarmu ta sanar mata kato6arar da Aiyaan yayi. “to Yaya ko su Munaya sunzo k'asarne?”. Anya kuwa Rabi'a, naga jiya mijinta na nan amma baiyi maganar zata zoba”. “ito da wannan dan wanann, amma ai bama fidda raiba”. “hakane”. cewar innarmu. Babu dad'ewa da zuwansu saiga gwaggon Haleematu da matan k'annen ta sunzo duba Abba, (dayake har yau bata dawoba ita). k'in gaisawa tayi da innarmu da mamansu yaa hameed, innarmu bata damuba, amma mamansu yaa hameed saida taja tsuka, babu dai Wanda ya tanka. Sukuma suka shiga suka ga Abban, dayake yau ana barin na jikinsa zuwa su duba shi. Koda suka fito harda kuka takeyi, matan k'aninta suka tafi amma ita saita zauna, kaf 'yan gidanmu babu Wanda yace mata danmi, kowama tasa ta isheshi aransa. ★★★★★ Tunda motocinmj suka shigo harabar asibitin sai kallo ya koma sama, 'yan gidanmu dakeda yak'in Galadima ne kowa tsumayen fitowarsa yakeyi, sauran jama'a kuma da 'yan dubiya son ganin wad'anda zasu fito sukeyi. Sai da aka bud'e mana sannan muka fito, suma su Harun duk sun fito. Su yaa Hameed suka taho garemu sunama Galadima sannu da zuwa, cikeda kulawa yake amsa musu. Kowannensu fuskarsa ta nuna farin cikin ganina, yayinda nikuma naketa faman zirar da hawaye. Cikin d'okin ganina Fauziyya tazo ta kama hannuna itada Safara'u, saina rungumesu na fashe da kuka, kukana ya karyar musu da zuciya suma suka fara, sauran 'yan uwanama duk suka taso gareni, dama duk sun zo, ni kad'aice wadda nake nesa. Saida baba k'arami yamana magana sannan suka sakeni, na matsa ina sharar kwalla na gaida iyayena, Munubiya ce kawai ban ganiba, ina share hawaye na tambayi tana ina?. Aunty khalisat tace “sunje ganin doctor itada yaa marwan, dan batajin dad'i itama”. Kaina kawai na jinjina, na k'arasa gabansu innarmu na durk'usa ina gaishesu, duk sun amsamin cikeda kulawa, da tambayata ya hanya?, nace “Alhmdllh”. Matan gidanmu kowacce kallona take da mamakin canjawata a cikin wata 1 kacal. Na katse musu tunani da tambayar d'akin da Abba yake. Aunty Ramlah ce taja hannuna muka shiga corridor d'in dazai sadamu da d'akin da Galadima yasa aka canjama Abba. A ciki na iske Galadima da Harun da Sauban, sai doctor da yaa Shafi'u yaa Hameed. Takun takalmanmu yasakasu juyowa suka kallemu, na zare hannuna daga na aunty ramlah ina toshe baki saboda kukan dake Neman kufcenin, taka wa nayi gaban gadon da Abba yake, na durk'ushe ina sakin kuka mai tsuma rai da zuciyar mai saurarona, tare da kife kaina jikin gadon. Kukana babu zuciyar Wanda bai karya ba, Galadima ya tako a hankali inda nake, hannayensa biyu ya saka ya kamoni na mik'e tsaye, fad'awa nayi saman k'irjinsa na kuma sakin wani sabon kukan. Bashida za6in daya wuce kar6ata, dan haka shima saiya saka hannayensa ya zagaye bayana dasu, ya d'ora ha6arsa saman kaina yana lumshe idanu da cije lips. kad'an-kad'an yake buga bayana alamar lallashi. d'ai-d'ai su yaa Hameed suka zare jikinsu suka fice daga d'akin, aka barmu mu kad'ai sai Aunty Ramlah da muka birgeta, itama ganin sun fita saita fice taja mana k'ofar. Munkai tsawon lokaci ahaka, saida na tsagaita da kukan sannan Galadima ya d'ago kaina daga jikinsa, hannunsa yasa yana gogemin hawayen fuskata, amma ya gaza cewa komai. sai girgiza min kai kawai yakeyi. Ajiyar zuciya kawai nake saukewa a jere, da hannu ya nunamin hanyar fita. Banyi musuba nabud'e k'ofar muka fito, ina gaba yana bina a baya. tafiya nake a hankali saboda juwar dake Neman fara hajijiya dani, burina kawai nakai inda 'yan gidanmu suke zaune akan kujeru nima na samu na zauna. Muna gab da k'arasawa wajen na dafe kaina, sai nayi baya luuuuuu. Da sauri Galadima dake bayanta ya tareta ta fad'o jikinsa, gaba d'aya 'yan gidanmu da mutanen wajen suka mik'e tsaye cikin ambaton sunan ALLAH. sosai Galadima ya tallafota jikinsa, yayinda wasu Nurses biyu suka iso da gudu domin kar6ar Munayar. Amma saiya hanasu yana daka musu tsawa da ambatar su kira Doctor. Basu ba kowama a wajen saida tsawarsa ta rikitashi....................✍🏼 *_Comments d'inku shike k'aramin k'arfin guywar rububutun nan wlhy, amma da tuni na ajiye saina samu lafiya🤦🏻‍♀, amma yanda kuke k'ok'arin Comments sai bana iya barinku banyiba😃, ina godiya kwarai da gaske, I love you all🥰🥰🥰🥰🥰🤝🏻👍🏻❤_* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_* *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻7⃣ ................Gaba d'aya ya rikice ya rikita Nurses d'in da jama'ar wajen, cak ya d'auki Munaya, gadonma da aka kawo masa domin d'orata ko kallonsa bai yiba. Wani d'aki suka nuna masa ya shiga da ita. Da sassarfa doctor dazai duba munayar ya iso, dan dogaran Galadima tasoshi gaba sukaje sukayo. Kai tsaye Galadima yace baya buk'atar namiji mace yakeso ta duba masa matarsa. Hak'uri doctor d'in ya bashi, sannan yakira wata likita mace mai suna doctor Farida. Isowarta yasaka Galadima da yay bake-bake a k'ofar bata hanya ta shiga. Duk yanda taso yabata waje tayi aikinta yak'i, gashi duk yabi yagama rikitata da tsawarsa. Doctor d'in da Galadima ya hana ya duba Munaya ne ya matsa kusada su harun yana fad'in “dan ALLAH sir Ku lalla6a yalla6ai ya fito danta samu damar aikinta, wlhy dukya rikitata”. Murmushi Nuren da isowarsa kenan asibitin aka masa bayani shima yayi, suma su harun duk murmushi sukayi. Nuren ya kalli baba k'arami yana murmushi, “Abbanmu inharfa bakai kamasa magana ba bawai zai fito baneba”. Shikansa baba k'arami murmushin yakeyi, koba komai hankalinsu Yakuma kwanciya da zaman 'yarsu inda suke tunanin anfi k'arfinta. Bayan doctor yabi zuwa d'akin, Galadima dake zaune, kan Munaya na bisa cinyarsa sai murza tafin hannunta yakeyi wai kozata farfad'o, yayinda doctor Farida ke k'ok'arin lik'a mata oxygen ita kuma”. Shima baba k'arami da k'yar ya lalla6ashi ya fito. Tsawon lokaci doctor Farida tana ciki bata fitoba. Galadima dukya damu, danma ankawo masa kujera ya zauna, amma sai jan tsuka yakeyi time to time. Hankalin 'yan gidansu Munaya ma duk a tashe yake, jiran fitowar doctor Farida kawai akeyi dan aji mike damun munayar. Innarsu Munaya kam gefe ta koma tana sharar kwalla, itakam batasan yazata misalta wannan tsakaniba, miji da 'ya'ya duk babu lafiya, Munubiya ma fa sunacan ana k'ara mata ruwa. Fitowar doctor Farida yasaka kowa mik'ewa anason jin bayani, Galadima dai yana daga zaune ya zuba mata idanu shima. Doctor Farida tace su kwantar da hankalinsu ta farfad'o, amma tamata allurar barci, yanzu tanason ayo gwajin jinin Munayar data d'iba. Galadima ya lumshe ido yana ambatar “Alhmdllh” akan la66ansa. Sauban ne ya kar6a suka tafi shida Sarkin mota lab d'in. Dr Farida ta kalli Galadima tana murmushi, “ranka ya dad'e zaka iya Shiga ka ganta yanzun”. Nuren ya kalli Galadima ya jinjina masa kai alamar yaje. Saida yaja wasu seconds sannan yamik'e cikin takun nan nasa na k'asaita da izza, duk idon jama'ar wajen akansa yake, yana birge kowa. d'akin ya tura ya shiga, ya taka har gaban gadon da Munaya ke kwance, idanu ya tsura mata, tayi wani fayau da ita, ya jawo kujerar dake wajan ya zauna, har yanzu idonsa na kanta, cikin cije lips da lumshe idanu ya d'ora hannunsa bisa sumar kanta da d'ankwalinta ya zame ta fito, saikuma yasaka d'ayan hannunsa ya shafi kumatunta, a kan la66ansa ya furta “sorry my friend, ALLAH yana tare da masu hak'uri kinji”. Daga haka bai sake cewa komaiba, ya janye hannunsa daga kanta ya mik'e ya fito. A k'ofar d'akin ya iske Doctor Farida tsaye, kallonta yayi cikin maganarnar tasa mai kama da an masa tilas yace “zata iya kaiwa wane lokaci bata farkaba?”. “Ranka ya dad'e inaga daganan zuwa kamar awa d'aya”. Kansa ya jinjina mata, bai sake magana ba yanufi d'akin da Abba ke kwance. ya Tatar da doctor d'in dake kula da Abban a d'akin. Da sauri doctor yabashi kujera ya zauna, k'afa d'aya kan d'aya ya d'ora ya Ciro waya a aljihu yana danne-danne. batare da ya kalli doctor ba yace, “kunyi gyaran karayar?”. Doctor yace, “eh ranka ya dad'e duk an gyara, saidai na hak'ark'arinsa yaso kawo matsala, amma Alhmdllh komai ya dai-daita”. “humyim, maganar bayanan danace a tattara minfa?”. “shima komai ready ranka ya dad'e ”. “o right, insha ALLAH zuwa jibi nakeson mu tafi, amma wai har yanzu bai ta6a farfad'owa bane?”. “ai ba'a sume yakeba, allurar damuke masace kawai takesakasa yawan barci”. d'ago ido Galadima yayi yana kallon doctor d'in, yace “amma danme ake masa?”. “ itace ke taimaka masa wajen rage masa rad'ad'in ciwukan, dan maganar gaskiya yana cikin matsanancin ciwo”. Cije lips Galadima yayi kawai, yace “ALLAH ya bashi lafiya”. “amin ya rabbi”. ‘cewar doctor. Daga haka suka fito shida doctor d'in. Inda Harun yake Galadima ya nufa, “brother yau ba zakaje aikiba kenan?”. Kallon agogon hannunsa Harun yayi, sannan ya kalli Galadima, “ka rikitamu ne ranka ya dad'e shiyyasa ban kula time ya tafi hakaba”. Murmushi kawai Galadima yayi amma baice komaiba. Harun yay musu sallama ya fita da nufin zuwa anjima idan yatashi aiki zai dawo. Su yaa Hameed sukai masa godiya da fatan alkairi sannan yatafi. Daddy ya kalli su yaa Hameed d'in yace ai kuma da tafiyar kukayi, karku makara wajen aiki”. A ladabce suka amsa masa da to, suna shirin barin wajenne saiga motocin su waziri sun shigo, dole su yaa hameed suka dakata. Waziri ne da matawalle, sai Garkuwa da baraya, sai kuma wasu manya-manyan 'yan majisar Sarki. dogarai duksun kasa sun tsare, wasuma zato suke sarkinne yazo da kansa. Su daddy ne suka musu iso har d'akin da Abba yake kwance, sosoi suka nuna tausayawarsu gareshi, sunja doguwar addu'ar samun lafiya da fatan alkairi ga Abba. Sannan suka Isar da sak'on Sarki. Sun d'an jima a d'akin suka fito da nufin tafiya, a dai-dai time d'inne kuma doctor Farida ta iso gaban Galadima cikeda sassarfa. Bakinta a washe tamkar gonar auduga. Wani dogari Na k'ok'arin dakatar da ita Galadima ya d'aga masa hannu alamar ya barta tazo. Cikin girmamawa doctor Farida tace “wannan asibiti da dukkan jama'ar cikinsa suna taya masarautar gagara badau murnar samun k'aruwa daga jikin gimbiya Munaya, insha ALLAH nanda watanni 7 dawasu satittika zata zama uwa, ma'ana tana d'auke da cikin wata 1 da sati uku”. Atare dogarai suka d'auki kabbara, Galadima dake tsaye baki bud'e cikin tsantsar mamaki ya kafe doctor Farida da idanu, sai kawai yashiga zame agogon hannunsa mai masifar tsada da k'yau ya mik'ama doctor Farida. Sauban yazo ya rungumesa, hakama matawalle. 'Yan gidansu Munaya sai suka koma 'yan kallo kawai, amma bakin kowa yakasa rufuwa. Doctor Farida ta kalli Galadima cikin mamaki da al'ajabi, “ranka ya dad'e ni Na cancanci wannan agogon mai d'unbin tsada kuwa?”. Wani murmushin Daba a cika gani Galadima yayiba ya saki, ya gyara tsayuwarsa yana fad'in “idan duk abinda na mallaka a duniya kike buk'ata zan baki shi, saboda wannan shine albishir Na farko da aka ta6amin Na farinciki a rayuwata, kifad'i dukkan abinda kike buk'ata inhar baifi k'arfina ba kafin nabar asibitinnan za'a kawo miki shi”. Kanta ta shiga girgizawa, kafin ta d'aga agogon ga mutane su gani. Mamaki ya cika kashe matan gidansu Munaya hassada da al'ajabi ya cika zukatansu, tunma ba'a haifi cikinba Galadima yake wannan rawar kan inaga an haifoshi?, Kansu bai kuma kwanceba saida sukaji waziri da baraya Na sanarda tasu k'yautar ga doctor Farida, hakama matawalle da Nuren. Doctor Farida fa ta rikice, itakam yau taga farar rana, (🙄idan ta ALLAH ake niya kamata abama wad'annan k'yaututtuka ma😏). Nuren da matawalle suka hau rabon kud'i a asibitin, tamkar basu San ciwonsu ba. Waziri kam d'akin da Munaya take kwance aka musu rakkiya, sun mata addu'a kafin su fito, kowa bakinsa a washe, wasukam ta cikin Na ciki kawai😳🤭. Kafin kace mi labari yagama zagaye asibitin, gidan Sarki kam kafin su waziri su Isa labarin cikin Munaya yaje. hakama Sauban ya kira su Momma ya guntsa musu, Momma saida tayi sujudar shukur. Abie bakinsa yakasa rufuwa, kamar daga sama sukaji yace “ALLAH ya inganta”. Dukda a hankali yayi maganar hakan bai hanasu ganin motsawar la66ansa ba, Khaleel dake kusa dashi yace “Lah Abie yayi magana Momma!!”. ba momma ba hatta da jakadiya sakin kwanon hannunta tayi ta waigo tana kallon Abie. Aunty Mimi ta tura laptop d'in gabanta tafad'o, hakama Samha wuntsilowa tayi daga kujerar datake zaune tayo inda gadon Abie yake. Gaba d'aya suka rufu akan abie, kowa yanason sanin gaskiyar batun Khaleel, murmushi Abie yamusu yana jinjina kai alamar gaskiyane, sannan a hankali yakuma furta “da gaske Khaleel yake”. Ai yau babu kunya Momma ta rungume Abie a gabansu aunty Mimi ta fashe da kuka mai ban tausayi. Aunty Mimi ta had'a momma da Abie d'in ta rungume itama. Jikin Samha har 6ari yakeyi takira Number Galadima ta Nigeria. Ya rako su waziri da zasu tafi kiran Samha ya shigo, bai d'auka ba, itakuma bata gaji da kira ba. Saida su waziri suka wuce sannan yaciro wayar a aljihunsa cikeda haushin wanene mai nacinnan. yana dubawa yaga Samha Ce. Murmushi yayi kawai sannan ya kirata da kansa, bugu d'aya Samha ta d'aga, kuka kawai ta fashe masa da shi, zuciyar Galadima tashiga tsitstsinkewa. tsawa ya daka mata yana tambayar lafiya?. Share hawayenta tayi, murya Na rawa tace, “Uncle Sam wlhy Abie yayi magana, yanzun nan da Uncle Sauban ya kira yace aunty gimbiya nada ciki sai Abie yace ALLAH ya inganta”.. Galadima ya ciro wayar a kunnensa ya kuma kallon number, tunaninsa wasune kawai keson masa yawo da hankali, ganin dai da gaske number Samha d'in ce saiya maida a kunnen, cikin sanyi murya ya kira ainahin sunan Samha, “Zeenah! banason wasan banza kema kin sani”. “wlhy Uncle ba wasa nakeba, ga Momma ma kaji awajenta”. Kafin yace wani Abu yaji muryar Momma namasa sallama, yanayin muryarta yasakashi lumshe idanunsa. Momma tace, “Muh'd! Yau ranace dabazamu manta da itaba a tarihinmu, k'yautar abinda kud'i baya saya, ALLAH kuma yabama takawa damar magana, narasa yanda zan musalta farin cikina Muh'd”. Wasu hawayene suka gangaro a kumatun Galadima, ga murmushi yak'i barin fuskarsa, cikin nutsatstsiyar muryarsa yace “Momma ko yanzu Ubangiji ya d'auki raina yagama min komai, Momma mizanyi duniya tasan ina cikin tsantsar farincikin da tunda nazo duniya ban ta6a riska ba?”. Dariya momma tayi, tace “godiyar ALLAH ta wadatar da komai Muh'd, lallai yarona zai zama baba”. Galadima yayi dariya yana goge hawayen fuskarsa, “Momma bama Abie wayarnan”. Cikin tsokana tace, “nawa zaka biya? kasan mu yanzu komai Na kud'ine”. Sosai yasaka dariya, har jerarrun hak'oransa Na bayyana. Dogaransa duk sun saki baki suna kallonsa, duk da bajin maganar da yake sukeba, tunda suke da shi basu ta6a ganin yana dariya makamanciyar wannan ba, Sauban kan ai hotuna yaketa masa bai saniba. “shikenan Momma, inhar baki had'ani da Abie ba kema kuwa d'iyarki bazata dawo India ba ashe?”. “a'a miyay zafi? indai takawa ne gashi”. Nanma dariyar Galadima yayi, Abie da tun d'azu yaketa murmushi shima saboda a Hans free momma tasaka wayar duk sunaji, a hankali yace Daddyn Unborn!”. Galadima baiji mi Abie ya fad'a ba, amma tabbas yana jiyo alamun motsi, da sauri yace, “Momma video call please ”. Mota ya bud'e ya shiga, Sauban ma ya k'araso dan kuma taya d'an uwansa murnar k'aruwar daya samu. tunda aka bayyana maganar cikin Galadima bai samu Kansa ba, balle su ke6e. Motar yashigo shima, ganin video call Galadima ya had'a dasu Momma saiya matso kusada shi sosai yana d'aga musu hannu. Momma tace, “ho autana ina ka shige wai?”. “momma ina zaki ganni nazama Abban Unborn”. Dariya sosai suka sanya, Galadima ya rankwashi kansa. Wayar aka saka kusada Abie sosai, a hankali yace, “lallai wad'annan iyaye akwai zumud'i dai”. Basuji miya fad'aba. Amma sungane ta hanyar motsin la66ansa. cikin zaro ido Sauban yace “Abie!!”. Sai kawai ya rungume Galadima ya fashe da kukan farin ciki. Humm masu karatu, nabama kowa damar k'iyasta wannan farin cikin a zuciyarsa shima😁😉. ★*★★*★*★★*★*★★*★ A lokacin da Galadima suke can suna waya dasu Momma Munaya ta farka, doctor Farida ta cire mata k'arin ruwan danya k'are. Ta kalli doctor Farida tace “doctor Abbana fa? karki cemin dai Abbana ya mutu Dan ALLAH?”. Hannunta doctor Farida ta rik'o, fuskarta d'auke da murmushi tace, “gimbiyarmu Abbanki nanan da ransa, insha ALLAH kuma zai tashi, kedai kici gaba da masa addu'a kinji”. Kai Munaya ta jinjina mata, sannan tace, “to zanyi fitsari”. Doctor Farida ta amsa da to, da kanta ta taimakama Munaya tashiga bayi, fitowa tayi tabata waje, saida ta gama sannan ta kuma taimaka mata ta fito. “doctor 'yan gidanmu fa?”. Murmushi Dr Farida tayi, cikin tsokana tace, “Gimbiya Galadima yakamata ki fara tambaya ai”. Murmushi Kawai Munaya tayi, amma batace komaiba, Dr Farida tace “to bara Na musu magana”. Babu dad'ewa saiga 'yan gidanmu nata shigowa, yanda kowanne fuskarsa ke a washe sai suka bani mamaki, nakasa hak'uri nace, “Abba ne ya tashi? kuke farin ciki haka?”. “shima insha ALLAH zai tashi 'Yar albarka”. Cewar innaro tana dariya. Ni duk sun kuma d'auremin kai da addu'ar da sukeyi suna fad'in ALLAH ya inganta. Mamansu Fauziyya tace minakeso akawo min naci. Nace, “banajin yunwa mama, ni sonake ma Na kuma ganin Abba”.. “karki damu, Abba yana barci ne, kedai kisamu kici abinci babynmu yak'ara k'ato kafin ki haifo mana”. Ban fahimci maganar ta Fiddausi ba, Dan naga awajen akwai masu ciki da yawa, aunty Ramlah, aunty Khaleesat, aunty Hauwa'u, Siyama, Zarah, aunty Raihana duk cikinsu ya tsufa, haihuwa yau ko gobe. Na kalli innarmu dake tsaye batace komaiba, murmushi namata, itama saita mayarmin, nace, “wai har yanzu Munuhiya ba a cire mata ruwanba?”. Mama Rabi'a tabani amsa da cewar “an cire, barci takeyi”. Cikin marairaicewar murya nace “ALLAH sarki Sweetheart d'ina, ALLAH yabaki lafiya”. Duk suka amsa da amin. Doctor Farida tashigo tana sanar musu ga Galadima nan zai shigo. 'Yar rige-rigen fita iyayena suka farayi, kowa yana jin nauyin suruki ya shigo ya iskeshi, ni dariyama suka bani, nayi murmushi ina komawa Na kwanta. Saida suka fita kaf sannan nafara jiyo takun takalminsa. Idanu Na lumshe kamar mai barci. Tunda ya shigo idonsa Na kaina, yacigaba da takowa gaban gadon, duk tunaninsa barcin gaske nakeyi, maimakon ya zauna saiya dafa gadon ya rankwafo kaina, da sauri da sauri zuciyata tafara bugu saboda kusantoni da ya keyi, fuskarsa daf da tawa tamkar zai had'e bakinmu, mikuma ya tuna saiya janye ya maida saitin goshina ya manna min kisses guda biyu a goshi da saman hanci. Cikeda mamaki Na waro manyan idanuna, kallon ido cikin ido mukaima juna, ya d'aga min gira d'aya. Saurin kauda idanuna nayi gefe. Shikuma yaja kujera ya zauna dab da fuskata yana murmushi. Munja wasu seconds sannan yasaka hannunsa bisa kumatuna ya juyo da face d'ina inda yake, kin bud'e idona nayi Na kallesa, bai damuba yace “yalla6iya dama haka kike da saurin cafke Abu?”. Babu shiri Na waro idanuna kansa, nace “yalla6ai mina cafke?”. Idanunsa ya d'an jujjuya alamar tunani, saikuma ya kalleni, har yanzu hannunsa Na tallafe da fuskata, yace “uhuumm mima kika cafke? Na manta ma”. Ya k'are maganar da d'age kafad'a yana ta6e baki. d'an hararsa nayi ina tura baki, mutuminnan ya iya rainin wayo. Yanzunma murmushin yamin, saikuma ya d'ora hannunsa saman shafaffen cikina mai kama da babu ko kayan ciki balle kayi tunanin akwai mutum. Da sauri Na rik'e hannunsa ina fad'in “ yalla6ai lafiya kuwa?”. Cikin basarwa yace “itace ta kawo haka, bakimin murna ba”. Nace, “Murna kuma? tami?”. Cikin d'age gira d'aya yace “Muhammad Sameer Saifudden yazam pah-pah”. d'auremin kai maganarsa tayi, Na yunk'ura a hankali zan tashi, mik'ewa yayi ya taimakamin Na zauna yana fad'in “yi da kula karkima jama'ar gari 6arna, dan akwai sarkinsu anan”. Waige-waige Na farayi, nidai banga kowa ba bayan mu biyun dake zaune, saina d'auka da kansa yake, na d'an ta6e bakina kawai. Shima saiya ta6e bakin yana komawa ya zauna. kusan mintuna biyu duk mukai shiru. Zuwa can nace, “nikam dai na dawo normal, kace musu su sallameni kawai”. Batare daya d'agoba yace “nafi buk'atar hakan, mi kikeso Sameer yamiki k'yauta da shi?”. “k'yauta kuma? akanmi?”. “Abie ya fara magana”. Babu shiri na wuntsilo daga gadon ina fad'in da gaske?”. Da sauri Galadima ya ruk'oni, jikinsa har rawa yakeyi, jina nai kawai bisa cinyarsa. “yalla6ai!”. nafad'a cikin zaro idanu, sai kuma na hau waige-waigen kar wanifa ya ganmu. Daf yamatso da fuskarsa kusada tawa, numfashin junanmu na sauka bisa fuskokinmu, na marairaice fuska tamkar zanyi kuka, yanda yasaka idonsa cikin nawa tsigar jikina dukta mimmik'e, jikina har tsuma yakeyi, amma tsabar muguntarsa yak'i ya janye, yakuma hanani damar da zan janye nawa. A hankali tamkar mai rad'a, yace “ki kula, domin abin cikin kwan yafi kwan dad'i my friend ”. ‘ ya k'are maganar da d'age min gira sama’. Lumshe idanuna nayi kozan sami sassaucin daina ganin abinda ke yawo a idanun Galadima. hakan yabashi damar d'ora bakinsa akan nawa, shima ya lumshe nasa idanun. Babu shiri na bud'e nawa saboda tsorata, ni Munaya mike damun wannan bawa yau? duk yanda naso kwatar kaina hakan ya gagara, dole na sallama yayi iya yinsa sannan ya sakeni. Zumbur na mik'e daga jikinsa ina sharar kwallar takaici, shima saiya mik'e yana karkad'amin d'anyatsa, ya matso daf dani a hankali ya furta “k'yautar farko kenan”. juyawa yay yafita yana murmushi da gyara zaman hular kansa. Na bishi da kallo ina maimaita zancensa na k'arshe, “k'yautar farko? Kamar ya k'yautar farko? mi yake nufi to?”. ban kai ga samo amsarba doctor Farida ta shigo tana murmushi. “ginbiyarmu yalla6ai yace abaki sallama kuje gida ki huta gaba d'aya”. Saboda Banason tafiyar, sai nace doctor jikina bai gama sakiba, ki Ce masa sai dare zaku sallameni kawai”. 'Yar dariya tayi, ta nunamin Galadima dake bakin k'ofa tsaye ya hard'e hannaye a k'irji. Baki na tunzuro gaba saboda borin kunya. Shikuma ya janye idanunsa yana ta6e baki. Doctor Farida ta bamu sallama, na d'auki alk'yabbata na saka, tareda d'aukar handbag d'ita, sai wani ciccin Magani nakeyi, shi da nakeyi danshi yawani share tamkar bai gane da shi nakeyi ba. Jinai ya sak'alo hannunsa cikin nawa, na kalleshi da sauri, saiya kannemin ido d'aya. Ja nayi na tsaya, shima saiya tsaya, ga mutane duk sun zubo mana idanu, kuma har 'yan gidanmu. tamkar zan fasa ihu nace, “yalla6ai ni dai wlhy ka sakeni, kai bakajin kunyar su innarmu ma?”. Yace “kai ALLAH dai ya shiryeka Sameer, yalla6iya Sameer najin kunyar su Innarmu fa, sai dai kuma yana gudun amasa gangancin abin cikin kwan ne”. Kallonsa nayi, “ wai minene wannan abin cikin kwan daka ishi mutane da fad'a”. Ya d'an d'ora hannunsa saman bakinsa alamar mamaki, “yamzu nan bakisan abin cikin kwan ba friend? Lallai news ya wuce dake, ina tayaki jaje kam”. Kuma kullemin kai yayi a duhu. Ita dai doctor Farida dake bayanmu sai kuma birgeta muke da bata dariyar salon namu. Mutane kam dake kallonmu tunaninsu koda doctor Farida muke magana, Dan bazaka ta6a d'auka Galadima ya iya zaro magana hakaba. nikaina mamakin dama yana magana mai tsayi irin haka nakeyi, narasa miya d'abbak'a wannan farin cikin nasa na yau?, duk da bawai yanata dariya baneba, fuskarsa nanan yanda take babu walwala, sai dai yau akwai sakewa tattare dashi, kuma yakan yawaita murmushi bakamar ko yausheba. Nidai nace, “dan ALLAH yalla6ai kayi hak'uri, wlhy bazan iya zuwa gabansu baba k'arami ahakaba”. Baice komaiba ya saki hannuna, amma munci gaba da tafiya kafad'a da kafad'a dashi. Wata kuyanga cikin kuyangin da uwargidan Sarki ta had'omu tai saurin tasowa ta kar6i bag d'in hannuna, ban musaba na mik'a mata, mutane sai gaishini sukeyi, nidai kunyama ta isheni, Dan wasu sun girmemin. Mun Isa gaban 'yan gidanmu, kowa ya taso yana k'ara min sannu da jiki, nidai sai ce musu make na samu sauk'i. d'akin da Abba yake muka shiga, hawaye suka cikamin idanu, Galadima ya ruk'o min hannu, kallonsa nayi saiya girgiza min kai alamar kar nayi. Bance komaiba na janye idanuna, sannan na k'arasa gaban gadon nafara tofa masa addu'oi, shima Galadima ya matso ya tayani, daganan fitowa mukayi, Galadima yakuma gargad'ar police d'in akan su kula sosai, inhar wata matsala ta biyo baya to suyi kuka da Kansu. Cikin girmamawa suka amsa masa da insha ALLAH hakan bazata faruba ma. Ni dai ina wajen 'yan gidanmu, jinake kamar karna tafi wlhy, amma innaro tace kartaji karta gani, nabi mijina naje gida na huta, suma sauran 'yan uwana duk gida zasu tafi hakanan, tunda dai iya k'ok'ari galadima tsaye yake akan komai na abban, dukkan kulawa yasaka ana bashi gwargwadon iko. Nidai sai tunzura baki nake su Fiddausi namin dariya. Muna haka Galadima ya k'araso wajen, cikin girmamawa yace yakamata suma 'yan gidanmu suje gida hakanan su huta, insha ALLAH Abba zai samu kulawa tamkar suna nan. Godiya suka shiga yimasa, innaro nata kwararamasa addu'oin gamawa da rayuwa lafiya, da samun afuwa shima ga mahaifinsa, ta k'are maganar da f'adin “ALLAH ya kawo mana kishiyata ko angona duniya lafiya”. K'asaitaccen murmushi Galadima yayi, a kan la66ansa ya amsa da ammin Granny ”. Daga nan wajen Munubiya muka nufa, suma 'yan gidanmu suka shiga dansu k'ara ganin Abba su tafi. Munubiya na kwance tana barci har yanzu ana k'ara mata ruwa, rungumeta nayi ina hawaye, yayinda Galadima da yaa Marwan suke gaisawa cikin mutunta juna, inajinsu sunama juna Congrat, amma ban fahimci na mineneba. Nace “yaa marwan wai mike damun sweetheart ne haka ta rame?”. Dariya yaa marwan yayi, yace “babynku ne”. “lah yaa marwan kana nufin tanada cikine?”. Kansa ya jinjina min. Cikeda murna na kuma rungume munubiya ina fad'in “ashe na kusa zama mummy”. Galadima ya kauda kai gefe yana murmushi kawai, shina yaa marwan sai k'aramar dariya yakeyi. Da k'yar dai na hak'ura na baro asibitin nan badan nasoba, suma 'yan gidanmu duk sun wuce gida. ***************** A mota sai zun6ire-zun6iren baki nakeyi, saboda haushin banso rabuwa da 'yan uwana ba yanzu, Galadima ya wani shareni. shikam dukya gajine, bai cika wahalar zirga-zirga irin hakaba, gashi dama bawani isashshen barci yasamuba jiya. Batare dana kalleshi ba nace “wai ina yaa Sauban ne?”. Bai d'ago daga latsa wayar dayakeyiba ya bani amsa da “suna tare da Nuren”. Da sauri na kalleshi danjin ya ambaci sunan Wanda nake son Sanin wanene shi?, cikin kwantar da murya nace “yalla6ai wai wanene Nuren? ”. Tambayar tabashi mamaki, amma saiya share ya d'ago muka had'a ido, kowa ya janye cikin basarwa. bai bani amsarba har muka shiga cikin masarautar...................✍🏼 Kuyi manage da wannan sister's🤗. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻 *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻8⃣ .........Tunda aka bud'e mana muka fito hadimansa sukayo caa akan mu, kowanne k'ok'arin nuna farincikin sa yake ga Galadima. Casuke ALLAH dai ya infanta mana, ranki ya dad'e ALLAH ya saukeki lafiya. Cikin tsantsar farinciki yake amsa musu, murmushi yak'i barin fuskarsa. Nikam zuciyata Ce ta shiga tsitstsinkewa, idan har Na fahimci inda zancensu ya nufa cikine dani kokuma wani keda cikin? Galadima Na kalla, amma saiyamin wani miskilin murmushi yana kauda idonsa, alk'yabbar jikinace kawai taima mutane katanga da ganin zufar data gama jik'emin jiki. Tun a falon farko Na dakatar da kuyangin da damuke tare, handbag d'ita Na kar6a nace suje nagode. cikeda girmamawa suka amsamin suka fita suna min addu'ar k'ara samun lafiya. suna fita na juyo ga Galadima, amma tuni ya shige d'akinsa. handbag d'in Na dungurar saman kujera nabi bayansa, hankalina bazai ta6a kwanciya ba sainaji gaskiyar lamarinnan. Na iske babu kowa a falonsa, Dan haka nashiga bedroom d'insa, ranar farko kenan dazan fara shiga bedroom d'in. babu kowa nanma, sai motsin ruwa dana jiyo a bathroom. Waige-waige nafarayi ina k'arema d'akin kallo, komai ya birgeni a d'akin, sai k'amshin mayen turarensa da ya mannema d'akin. karaf idona ya sauka ga takarda kusada kayan daya cire, mik'ewa nayi Na d'akkota, Na dawo Na zauna. cikin nutsuwata nafara karantawa, nai mugun waro idanu ina fad'in “wlhy impossible, abindama bazai ta6a yuwuwaba kenan” sai kuma Na fashe da kuka. Dai-dai lokacin Galadima ya fito daga bathroom, sanye yake da rigar wanka fara, ahankali ya ringa takowa idonsa a kaina, sai dai fuskarsa a d'aure take tamkar bashine cikin walwala ba a asibiti. Bai k'araso inda nakeba ya tsaya a tsakkiyar d'akin ya cigaba da goge ruwan kansa zuwa fuska hankalinsa kwance. a harzuk'e nayo Kansa ina cigaba da kukana, naja birki a gabansa, da d'anyatsa Na nuna masa takardar, har yanzu kuma kukan nakeyi, nace “wannan cikin a jikin wa ake nufin yake?”. d'auke fuskarsa yayi daga kallona yana wani lumshe idanu, batare daya bani amsa ba ya taka zuwa wajen mirror, cikeda izza yace “sunanwa kika gani a jikin takardar?”. Da sauri Na ruk'o bathtub d'in jikinsa, cak ya tsaya, murmushin gefen baki yayi, saikuma ya kuma d'aure fuska sannan ya juyo yana fuskanta ta, inda Na rik'e ya kalla yana fad'in “kona kwance miki igiyar ne?”. Sakin rigar nai da sauri ina share kwalla, cike da tsiwa nace “aini ba 'Yar iska bace ba”. Shikuma cikin gatse yace, “amma kikayi ciki?”. Hannu na aza akaina nakuma fashewa da kuka, “wlhy koma mi za'ayi sai dai ayi bazan haifi wannan cikinba, aiba haka mukayi da kaiba, kawai daga auren Contract sai aganni da ciki? ka tabbatar saina zubar dashi yau d'innan, dan bazanje gidan miji da agola ba, ba kuma zan haifi d'ana Na bari gidan wani ba matar uba ta kashemin”. Da k'yar ya iya danne dariyar dake k'ok'arin kufce masa, yay saurin cafko hannuna saboda zaburar danayi xan fita. “k yi ahankali karkimin asarar abin cikin kwan fa”. Wani bak'in cikine ya turnuk'omin, Na harzuk'o masa da masifa amma saiya wani tsare gida, dolena Na had'iye maganar nacigaba da kukana. Shikuma ya watsa mini harara yana jan tagwayen tsaki, sannan yaja da baya yakoma bakin gadonsa ya zauna. Durk'ushewa nayi saman carpet d'in gaban gadon Na fashe da kuka mai tsuma rai ina rok'onsa. “dan girman ALLAH ka kaini a zubda cikinnan, kafa tuna da Girman alk'awari, a auren yarjejeniyarmu babu wannan, aikin had'in guywa ka nemeni muyi, kaifa ka tabbatarmin da zaka kasance mai cika alk'awari aranda Na kwana biyu a masarautarnan, miyasa yanzu zaka kasa cikawa? kacemin a matsayin kuskure abinda yafaru ranar ya faru, dukda zuciyata Na cike da bak'in cikin faruwar tasa haka Na hak'ura Na danne Na yarda dakai, ka taimakeni mu rabu cikin salama batareda d'ayanmu ya cutuba, karka k'ask'antar da rayuwata saboda kana ganina mace kuma talaka wadda take k'ark'ashin mulkinka, kamin adalci Dan girman ALLAH Muhammad Sameer”. Tunda munaya tafara magana Galadima ya tsaya daga k'ok'arin fara shafa man da yakeyi, idanunsa ya tsura mata, dukkan maganarta ta shigesa, dukda yana k'aunar cikin dake jikinta shima baiso gudan jininsa yazo ta wannan hanyar da babu soyayya tsakaninsa da mahaifiyar d'ansa ba, sai dai wayonsa ko dabararsa bazai ta6a canja k'addararsu ba shi da ita. da k'arfi ya cije lips nashi tamkar zai hudasu da hak'ori. Ya mik'e tsaye yana mai fidda huci mai zafi, takawa yay zuwa jikin window n d'akin, ya zuge labilan yana kallon waje, bayi keta kaikawonsu hankali kwance, dukda kasancewar rana ta take. ya maida labilan ya rufe Yakoma takowa tsakkiyar d'akin yana fad'in “tabbas ni Muhammad Sameer mai cika alk'awarine, kuma dukkan alk'awarin Dana d'auka miki ina k'ok'arin cikasu, sai dai nayi kuskure d'aya a cikin AUREN YARJEJENIYA, Na manta da babbar rahamar da ubangiji yake shinfid'awa ga dukkan wasu ma'aurata dazasu iya killace Kansu a matsugunni d'aya, Na manta da ko babu aure tsakanin mace da namiji inhar zasu kasance waje d'aya shaid'an yakan iya zama Na ukunsu ya sakasu aikata sa6o, balle mu da Muke ganin akwai igiyar aure a tsakaninmu, gaskiya kika fad'a, munyi yarjejeniyar aure domin gano mak'iyanmu bata zama Abu d'aya ba, amma kuma sai bamu d'auki matakan dazamu nisanta kawunanmu ba, daga ni har ke bamu Isa hana ubangiji ikonsa ba akanmu, tabbas ALLAH shidane bada gangan Na kusancekiba a wancan lokacin, sannan bansan ciki ya shiga jikinki ba, to mizaisa kizo ki titsiyeni kina min bore akan zubda shi. Bara kiji Na tabbatar miki yarinya, koda ace ta hanyar aikata zina Na Samar da wannan cikin inason abuna, kuma baza a zubarmin ba, ballantana sadaki Na biya d'unbin mutane suka shaida ke matata ce, mu uku kad'ai mukasan da wani Auren Contract. Dan haka kima nutsu idan zaki nutsu, kamar yanda kikace Duk abinda za'ayi saikin zubar da ciki ko? to Nima duk abinda zai faru saidai ya faru, babu ubanda ya Isa yasaka a zubar da cikinnan, sai dai idan Wanda yabani ne ya kar6a banida ikon hana wannan, idan kin gadama kici gaba da duk abinda kikeso har k'udirin zubda cikin, ni kuma Muhammad Sameer ina mai miki rantsuwa da ALLAH saina nuna miki ainahin color d'ina”. ‘ya k'are maganar da buga yatsunsa biyu suka bada sautin d'ass! d'ass!! A saitin fuskarta’. Fita munaya tayi da gudu daga bathroom d'in tana kuka, ahaka ta isa bedroom d'inta ta fad'a saman gado. Shi kuma tana fita yaja wani wawan tsaki ya fad'a kan gado yana dafe kansa dake sara masa. ga wata yunwa dake cinsa, shi saima yanzu ya tuna ko breakfast basuyiba suka fita, tsaki kawai yaja yana jawo wayarsa. number Nuren ya kira, bugu biyu ya d'aga yana tsokanarsa da fad'in “ho angon k'arni”. Galadima ya danne 6acin ransa, dan baya buk'atar kowa yasan wannan matsalar data kunne kai tsakaninsa da Munaya, muryarsa a sake yace “kun gama ne?”. “eh mun kammala, saidai kuma baka fad'i dawa-dawa za'ama visa ba cikin 'yan gidan nasu?”. Ya cije lips nashi yana gyara kwanciya, “tokai dawa yaka mata kake ganin zasu tafi?”. “eh, indai tanine gaskiya yakamata ace cikin k'annensa d'aya yaje, sai kuma mummynsu gimbiyarmu itama, tunda kaga itace first wife nashi”. “Okay hakan yayi, zuwa dare sai muje gidan muji yanda zasuyi, nasan kai dai bazaka shigo nanba, please kabama Sauban Abinci ya shigo mana dashi, dan ko breakfast My mata batayi ba”. “kai brother amma wannan sakacine ai, gashi ba ita kad'aiba?”. “wlhy Na mantane, saboda kaga ai yanayin da take tun barinmu gidan, inaga zanma inno magana a bamu mai abinci kawai”. “hakan zaifi kam, bara Na bashi ya taho yanzu kawai, amma zuwa anjima fa saika fito mun had'u”. “okay babu damuwa”. Yana yanke wayar kiran papi Na shigowa, fuskarsa d'auke da murmushi yay picking. cike da girmamawa yace “ran papinmu ya dad'e tare da k'yak'yk'yawan aminci”. “tunda kamin laifi fa ai dole ka faramin da dad'in baki”. Murmushi Galadima yayi har sarki Abdul'fatah na jiyo sautinsa, yace “a gafarceni ranka ya dad'e. ina fatan kuna cikin k'oshin lafiya kaida inno da dukkan ahalin masarautarka?”. “Alhmdllh Muhammadu. sai kuma wasu k'yawawan albishir suka riskemu a wannan rana. to ALLAH ya inganta, ya sauketa lafiya, shi kuma mahaifinka ALLAH yaci gaba da d'orar da lafiyarsa”. “Amin ya rabbi ranka ya dad'e ”. “Muhammad mikuma ya faru da sirikinka haka mara dad'in ji?”. “humm, ranka ya dad'e bansan miya sakoshi cikiba shi kuma?”. Murmushi mai sauti papi yayi, ya gyara zamansa akan kilisarsa, cikin nuna kulawa yace, “akwai abinda bamu saniba ne kawai, amma a fiddashi daga k'asar kafin mu fara wani yunk'uri”. Kamar Galadima na gabansa yashiga jinjina kansa, “to insha ALLAH zuwa gobe da daddare idan ALLAH ya kaimu zasu wuce". “hakan yayi, aci gaba da hak'uri dai kaji Muhammad, hak'uri jarine, jarabawa kuma tsanice ta zuwa wajen nasara, ALLAH yayi muku albarka”. “amin ranka ya dad'e, nagode sosai”. “yaushe zaku shigo?”. Murmushi Galadima yayi, hakan yana nufin kakansa nason ganinsa kenan, a ladabce yace “dasun tafi insha ALLAH ”. “ALLAH ya kawoku lafiya”. Tunda suka katse wayar saiyayta sauke ajiyar zuciya, koba komai ya sami nutsuwa akan wayar dasukai da papi. tashi yay ya k'arasa shafa man, sannan yasaka kayan da bazasu takurashi ba. Falonsa ya fito, abinda ake nunawa a tv ya d'auki hankalinsa sosai, ana cigiyar d'iyar Minister Ce, wai an nemeta an rasa tun a daren jiya. Akan la66ansa ya furta “Nuren!” Sai kuma yayi murmushi kawai ya kwanta saman doguwar kujera. A haka Sauban ya shigo ya sameshi da sallama, sai bayi buyu dake binsa a baya d'auke da ledoji. Galadima ya bud'e idanunsa yana kallonsu amma bai tashiba, bayan bayin sun ajiye suka zube sunama Galadima barka da hutawa, murmushi kawai ya musu ya d'aga musu hannu. Sauban yabasu izinin tafiya. Zama Sauban yayi a kujerar dake kallon Galadima, “kai yau ina cikin nishad'i wlhy yaa Sam...” Kallonsa Galadima yayi yana d'an murmushi, amma baice komaiba. Sauban yace “yaa Sam... Aunty gimbiya fa?”.. Galadima yace “barci takeyi”. “tofa Unborn babynmu yazo da sabon salo kenan”. Hararsa Galadima yayi, ya mik'e yana dariya ya shige bedroom. Galadima ya girgiza kai kawai yana tashi zaune. ledojin ya duba dan ganin mi suka sayo?. Abinda yasan zata iya ci ya d'auka ya fita. Saida ya d'anyi jimm a k'ofar d'akin sannan ya shiga da sallama, har yanzu tana a kwance tana kuka, lips d'insa ya d'an cija sannan ya ajiye abin hannunsa saman table d'in dake gaban gadon, idanu ya tsura ma bayanta nawasu 'yan seconds, ko alk'yabbar bata cireba, zama yayi a bakin gadon kusada ita, amma ya juya mata baya. Tun daga shigowarsa har zamansa tana jinsa, amma ko motsi batayiba, kusan mintuna 3 suna zaune a haka, ganin batada niyyar tashi ko kulashi ya sakashi juyawa yana kallonta, gyaran murya yayi sannan yace, “tashi kici abinci”. Shiru tayi ta shareshi, ko motsima bata yiba. Tsawa ya daka mata, babu shiri ta tashi zaune, jikinta sai rawa yakeyi, tunba yanzuba munaya akwai tsoron tsawa, bata barin saita kwana amma batason amata tsawa. Shi kansa yayi mamakin tsoratar tata, ya watsa mata harara yana kwafa, sai kuma yaja tsaki, alk'yabbar yacire mata, sai hawaye take zirarwa, bai kuma cemata uffanba ya bud'e abincin ya ajiye a gabanta, kafeta kawai yayi da idanu, hakan saiya tasirantar da tsoronsa a zuciyarta, dan haka tafara cin abincin, tanayi dai hawaye na zurara, cikin nata bamai tsurfa baneba, komai ci take hankali kwance, sai dai laulayi na ciwo. Dolenta ta saki jiki taci abincin, danya kafeta da idanu ga fuska cid'in-cid'in, duk jarumtarka dolene kaji shakkarsa. Kallo d'aga tamasa ta janye idonta, shi kuma ya harareta yana fad'in “kin k'oshi ne?”. Kanta ta jinjina masa tana matso kwalla. baice komaiba ya sauke sauran abincin k'asa, sannan yace “sauka kije kiyi wanka”. Baki ta bud'e zatayi magana ya dalla mata harara. sauka tayi tana k'unk'uni akan la66a. yana kallon motsin la66an nata, sai dai bayajin mi take fad'a. Yau kam Alhmdllh taji dad'in jikinta, ko k'arin ruwan da aka saka matane yasakata jin kwarin oho, ruwa mai d'an d'umi ta tara tayi wankan, tanayi tana hawaye, itafa ko mi zaiyi ba masifaba bazata bar cikinnan ba, babu yanda za'ayi ta reni ciki ta haifeshi sannan yazo daga baya ya saketa, bazata d'auki wannan rainin hankalinba, su maza a kullum d'aukar mace suke mai k'arancin tunani, kowane yayin rashin mutuncinsu suka kwaso saiya k'are akan mata, wlhy akan cikinnan tata d'aga masa hankali kenan harsai ya amince an zubar dashi sannan, kuma ana zubarwa zata k'ara gaba, mahaifinsa kam kobasa tare insha ALLAH zata cigaba da masa addu'oi ana aika masa. Jin shiru tak'i fitowa ya sakashi mik'ewa, bai wani kwankwasa ba ya bud'e k'ofar bathroom d'in kawai, danshi zatonsa ba wankan takeba ta tsaya kukane. A birkice munaya ta kalli k'ofar, ganin Galadima tsaye yana kallonta ta fasa k'ara, yay hanzarin ida shiga bayin ya rufe bakinta da tafin hannunsa dankar ta tara masa jama'a. Juyawa tayi ta ruk'unk'umesa, tare da saka hannayenta ta zagaye bayansa ta manne k'irjinta da nasa, ita duk bata son yaga jikinta ne😂😝. Shima fuskantar hakan da yayi ya sakashi sakin murmushi, saiya saka hannunsa biyu ya zagaye bayanta ya manneta sosai a jikin nasa. Shiru sukayi nawasu seconds, tana sauke ajiyar zuciya shima yana saukewa, saboda yanason ganin yanda zatayi saiya fara k'ok'arin janye jikinsa itama zai janye ta. K'ank'ameshi tayi ta fashe da kuka, jiyay tamkar ya kwashe da dariya, amma saiya daure, cikin dakiya yace, “malama sakeni mana? konaci bashinki ne wai?”. Cikin dasashshiyar muryarta datasha kuka tace, “to kabani zanina da hijjab na saka”. “to kin k'udunduneni ta ina zan iya baki wani zani? sakeni saina baki”. Kafad'a ta nok'e alamar tak'i. Murmushi Galadima yayi, ya shafa bayanta cikin murya k'asa-k'asa yace, “idan an hanani ganin can ai gashi ina kallon nan”. Da sauri tayi wata wulk'itawa ta koma bayansa ta 6uya. Kansa ya dafe yana fad'in “yau Sameer kaga ta kanka, ranar farin cikinka sai saka maka ciwon kai da zafin kai akeyi, wai ke yalla6iya mikike 6oyemin daban saniba ne?”. Baki ta murgud'a masa tana fari da idanu, dayake ba ganinta yakeba baisan hidimar datakeyi ba. K'ok'arin juyo da ita ya farayi amma tabi ta kanannad'e shi, rasa yanda zai mata yayi. yakula yarinyarnan 'Yar daruce kawai. zaninta ya jawo ya mik'a mata, saida ta tabbatar ta d'aura sannan ta sakeshi, yana juyowa ta juya masa baya ita kuma. Baice komaiba ya ta6e baki ya fice daga bathroom d'in. Harar bayansa tayi ta na fad'in “ALLAH ya isana”. Nace Humm.😏 Fita yay daga d'akin gaba d'aya, tunda dai yasamu taci abincin, harya kai k'ofarsa ya tuna batasha maganinta ba, dawowa yayi da baya. Ita kuma motsin fitarsa dataji yabata kwarin guywar fitowa. Shigowarsa tasata kwakumar hijjab ta saka, bakinsa ya ta6e ya wuce wajen handbag d'inta batare daya kalleta ba. Magungunan ya fido, ya zauna bakin gadon, “kizo kisha magani”. ya fad'a cikin k'asaitarsa. 6ata fuska tayi, tace “babu amfanin tattalin abinda za'a zubar ai”. Lips d'insa ya cije, sai kuma ya ajiye drugs d'in yana kallonta, mik'ewa yayi ya taka inda take, a bayanta ya tsaya, fisgota yayi ta fad'o saman k'irjinsa, saida ta rumtse ido dan zafin dataji, ya matso da fuskarsa daf da tata, a wani yanayin data kasa fassarawa yace “adadin nawa kike buk'atar na biyaki danki barsa?”. Rik'esa nayi da k'yau gudun karna fad'i, na janye idona dake cike da kwalla daga cikin nasa, “Bana buk'atar ko sisinka yalla6ai, cikinne kawai bana buk'ata, kuma bazan raineshi ba balle nakai ga haifeshi”. Wani murmushi mugunta yayi, sanan ya sakeni tamkar zai hankad'ani, mikuma ya tuna oho masa, saiya kuma damk'e hannuna, muryarsa a kausashe yace “wlhy idan kinga baki haifi cikin nanba to sai dai idan wanine a cikinmu numfashinsa yabar gangar jikinsa, sai kuma idan ubangiji ya kaddara Shiba mai Shak'ar iskar duniya bane, dan bani da hakk'in kowa, ubangiji kuma bazai barki ki shiga nawa ba”. yana gama fad'ar haka ya saki hannuna yafice daga d'akin baki d'aya. Yariga yasan zai fuskanci abindama yafi haka daga munaya, shiyyasa bai zafafama zuciyarsa akan wannan rikicin nata ba, shi babbanma burinsa yanzu Abbanta yabar k'asar nan, danya samu damar gudanar da aikinsa yanda ya kama ta. Da wannan tunanin ya dawo d'akinsa, ya iske Sauban kwance wai zaiyi barci, hararsa yayi yana fad'in “ kama tashi, time d'in zuhur yayi. Yana fita na raka bayansa da harara ina murgid'a baki, “oho dai, koma mizaka fad'a ka fad'a, nima ai bani tare da hak'k'in kowan, ALLAH kuma bazai baka damar danne nawaba, sokake nazama shashar mace ko? munyi auren contract batare da sanin iyayena ko naka ba, kazo kamin ciki na haifa maka ka sakeni na koma gidanmu, katashi da riba biyu kenan, nikuma babu ko d'aya sai bak'incikin danakema iyayena tanadi da kaina, Galadima ko a matanma ai _AKWAI BANBANCI?_ wlhy. gaskiyane Munaya, rik'e darajarki shine 'yancinki😄👍🏻. ******* Bayan sun fito massalaci sukejin labarin wai an rasa inda Muftahu yake, a safiyar yau aka samu motarsa a bud'e, sai kuma agogonsa da takalminsa d'aya a k'asa alamar da k'arfin tsiya aka saceshi. Hakan yasaka aka kama dogaran dake tsaron k'ofa ta uku, dan anga alamun tanan aka fita dashi. Dukda Galadima najin haushinsa saida hankalinsa ya tashi, dan haka suna shigowa ya d'au waya ya kira Nuren. Nuren na d'aga wayar Galadima yace, “Nuren Muftahu, kaine ko?”. “Muftahu kuma? nine naimi?”. “A daren jiya an rasa Wanda ya bar masarauta dashi”. “humm brother, dukda muna ganin Muftahu cikin masu mana zagon k'asa banta6a tunanin saina d'aukeshi zan gane hakaba, wlhy bani bane”. “ya salam”. ‘galadima ya fad'a cikin dafe kai da cije lips, wayar ya yanke ya Shiga safa da marwa, yarasa wazai hararo. Yana cikin wannan halin saiga harun shima a rikice, kowa yasan su ukunnan abokan junane, kuma akwai shak'uwa tsakaninsu, matawalle ne dama bai cika shiga cikinsu ba, saboda mama Fulani Na hanashi tun yana yaro, a cewarta shine d'an Sarki mai mulki, kuma shine mai jiran gado, darajarsa datasu Galadima ba dai-dai takeba, wannan hud'ubar ce tamasa tasiri sosai, amma yanason 'yan uwansa har zuciyarsa. “galadima shin kaji kuwa mike faruwa a masarautarnan?”. Cikin damuwa Galadima yace, “Harun su waye da wannan aikin?”. “kowa abinda yake tambaya kenan Sameer, Muftahu bashida wani abokin fad'a”. Hankalin Galadima kuma tashi yayi, shi duk damuwarsa karda a cutar da Muftahu ta dalilinsa, tunda ya kula duk wani makusancinsu shine abin harin mak'iyansa. shifa baima yarda ba Nuren bane da wannan aikin, dan yasan halinsa sarai, dolene kuwa yafita wajensa yanzunnan. Harun yace bara yaje, suna son akai report gidan radio da television. Jin jina kai Galadima kawai yayi, shima ya shige ciki danya shirya. Tun safe an sanarda jami'an tsaro 6atan Muftahu n, kuma suna a kan aikinsu. ★★★ Yunwar da yakeji tasashi bayan yayi shiri ya samu fresh milk yasha kawai, sannan yafito, d'akin Munaya ya lek'a, saiya isketa baje a gado tana shak'ar barci, baiyi yunk'urin tashinta ba yafito. Har dogaransa sun taso yace suyi zamansu su huta, zai fita shida Sauban, cikin damuwa sarkin mota yace, “kayi hak'uri ranka ya dad'e, koda nine kawai mu fita, Mai martaba ya sanar yau a fada kar'a sake barin wani d'an gidannan yafita wani waje shi kad'ai”. Kallonsa Galadima yayi, kamar zaiyi magana saikuma yafasa ya bud'e mortar da kansa ya shiga, batare da ya jira an bud'e masa ba. Da hannu sarkin mota yayma sauran dogaran nuni da su biyosu a baya idan sun tafi. A wani waje suka had'u da Nuren, Nuren ya fito daga motarsa yadawo inda Galadima yake, sai sarkin mota yafita yabasu waje kawai. Galadima yace “please idan kaine ka sakeshi”. Da mamaki Nuren yace, “wai Muftahu n dai? am telling you banida alak'a da d'aukarsa. yarinyar Minister ce kawai a hannuna”. “innalillahi, wlhy Nuren inajin tsoro, karsuje su cutar dashi”. “Sameer! nifa ina zargin kawai ya had'a baki da wasune suka kamashi dan yayi wasa da hankalinmu”. Idanu Galadima ya tsurama Nuren tamkar yana hango gaskiyar maganarsa, ya saki wani guntun murmushi, sannan ya gyara zamansa yana fad'in “well, koma minene dai zai fito ai”. Nuren yace “ni kaga dama kabar zancen wani Muftahu n banza can, way note mu wuce gidan sirikanka kozamu samu wasu evidence daga canma akan Accident d'innan”. Agogon hannunsa ya kalla, sannan ya kalli Nuren d'in alamar suje. Anan Nuren yabar motarsa suka tafi ata Galadima, saida suka fara tafiya Galadima ya lura da mototin dogaransa a bayansu. d'an murmushi yayi yana kallon Sarkin mota, yace “sarkin mota an karya min doka kenan?”. Sarkin mota daya fahimci Galadima yagane dogarai Na binsu sai yayi 'yar dariya, yace “ka gafarceni ranka ya dad'e, bazai yuwu mu barka ka fita kai kad'aiba ai, dan fitarka babu kowa tafi ta kowa had'ari a masarautarnan, mai martaba ma nasan saboda kaine ya saka dokar ai”. Galadima baice komaiba sai murmushi dayayi, Nuren ma murmushin yayi, sannan yace “amma kamar bayan motar dogaranka akwai wata bak'ar mota Na bin tasu?”. Galadima ya juya shima, tabbas anabin motar dogaran a baya, “sarkin mota su wucemu, karsu tsaya”. “To ranka ya dad'e”. Bayan sarkin mota ya sanar musu suka wuce su Galadima, motarma ta wuce, da kallo Nuren da Galadima suka bita, Nuren yay hanzarin d'aukar motar hoto a wayarsa. “humm da alama suna zaton kana d'aya daga cikin motocin canne”. Murmushi Galadima yayi, a k'asaitarsa yace, “kokuma suna son wasa da hankalinmu ba”. Da mamaki Nuren yace “kamar ya?”. Murmusawa Galadima ya kuma yi, ya kwantar da kansa jikin seat yana lumshe idanu, “Nuriddeen! Sameer ya wuce tunanin dukkan mai tunani, kai tsaye ba'a gane manufar zuciya, kwanji ko dama basu ke nuna k'arfin ikon mai ikoba, nazarin komai daki-daki da iya sarrafa duniya a yanda tazo shike nuna k'arfin gwarzan taka, mazantaka ba'a shaidata a fuskar namiji, duk lokacinda kai gamo da nama, kud'i, mata bisa hanya, karkayi rawarkan d'auka ko murnar ALLAH ne ya baka, zata iya yuwuwa tarko aka d'ana maka, shi k'yawu had'arine, 6oyeshi kuma nagartace, maiyi baya fad'an zaiyi, sai dai aga aikinsa a k'asa, tasowar iskar hadari bashi ke nufin ruwan zai zuba ba, watak'il sunan wannan iskar gyara kayanka. Dalili da dalilai basa ta6a saka zuciyar Wanda yake nema ta raunana, time d'in da zan nunama mak'iyan mahaifina d'an zaki ya girma yayi, sun durk'usar da shi a k'asa batareda tunaninsu yabasu ya haifi Raina kama ba, Su cigaba da raina aikin Muhammad Sameer daga k'arshe kuma saisuga gayya, tafiyar hawainiya bashike nufin gazawar kuzarinta bane, lokuta da dama hanzari kan katse igiyar cikar buri, a sannu kowa zai fahimci wanene *_RAINA KAMA....._*👎🏻 Ba Nuren ba hatta da sarkin mota maganganun Galadima ya shigeshi, tabbas mutane dayawa sunama Galadima kallon mutum mai yawan sakaci da rashin ho66asa, koshi yana d'aya daga ciki, amma wannan zantukan nasa sai suka sakasu a rud'ani, kenan akwai abinda sud'in basu saniba........... Dole tunaninsu ya katse saboda isowarsu gidansu Munaya. Fita sarkin mota yayi yanema musu iso, babu dad'ewa saiga baba k'arami ya fito, sarkin mota ya bud'ema Galadima, yayinda Nuren ya bud'e da kansa, zuciyarsa sai jujjuya hannunka mai sandar Galadima yakeyi. Dukda baba k'arami yayi mamakin zuwan Galadima haka ya danne, yaymusu k'ar6a ta girma, sannan suka shiga cikin gidan. Gidan tsitt tamkar babu mutane, saikace ba gidannan bane mai kama Dana 'yan dambe😂, (yo kowa Na tsoron a korashi gidansu🤣😝). A falon daddy aka musu masauki, dan danan aka cika musu gaba da kayayyaki, baba k'arami ya fita domin basu damar cin wani Abu. Babu abinda suka ta6a, dukda kuma Galadima ma yunwa yakeji, a haka daddy da baba k'arami suka dawo. Daddy yace “anya kuwa wannan d'an namu yana d'aukar gidannan matsayin nasu?”. Murmushi Galadima da Nuren sukayi, Galadima yace “sosaima daddy”. Baba k'arami yace “ta INA zamu amince da haka kuwa, bayan inada tabbacin ko ruwan gidannan Baka ta6a sha ba”. Kunya Ce ta kama Galadima, sai kuma yaga bai k'yautaba, ya rissinar da kai yana fad'in “amin afuwa zan gyara”. Mik'ewa baba k'arami da daddy suka kumayi, “to mun bada dama ta biyu”. cewar Dady yana dariya. Bayan fitarsu Nuren ya bud'e kulolin shima yana dariyar, danbun shinkafane daya samu nutsuwa ta musamman, sai k'amshi mai dad'i yakeyi, daga Galadima har nuren saida kwad'ayin cin abincin yazo musu. Kallon Galadima Nuren yayi yana d'aga gira, Galadima yay murmusa tareda fad'in “kadaiji kunya”. “kaima jinta zakayi yanzu, dan nasan ci zakayi”. Yau dai kam Galadima yaci abincin gidansu Munaya, kuma gashi girkin innarsu, babu kunya sukaita zuba Santi shida Nuren sunama juna dariya, Galadima harda su6utar baki yana fad'in “amma my mata muguwace, bata ta6amin irin wannan ba”.🙀 Mi Nuren zaiyi inba dariya ba🤣, su Galadima anji dad'i har kwalwar kai Baki ya bud'e😂😝. Saida suka mammala tsaf sannan su baba k'arami suka dawo, sunji dad'i dasuka iske sunci. Daga nan sukayi gaisuwa, su baba k'arami suka d'ora da godiyar d'awainiyar Abba da Galadima ya d'auke musu. Murmushi kawai Galadima yayi. Nuren ya gyara zama, a ladabce yamusu bayanin son fidda Abba da Galadima kesonyi, dan likitoci sunce ana buk'atar kulawa saboda karayar hak'ark'arinsa data k'ugu, “to yanzu haka dai angama setting d'in komai gameda tafiyarsa, har asibitin daza'a kaisa, visa d'insa da komai, sai dai anason tafiya da mutum biyu a cikinsu, mi kuka gani akan Wanda za'aje da shid'in?”. Daddy da baba k'arami suka kalli juna, summa rasa wane irin farin ciki zasu nuna dan Galadima yasan sunji dad'i? sunta jero masa k'yawawan addu'oi, kafin daddy yace “ai kawai sai atafi da jafaru da Ai'sha, dan bai kamata mutafi mu duka ba gida babu kowa, dukda akwai su Anas, gakuma su Hameed zasuke zagayowa, amma hakan yafi dai. Duk sun gamsu da hakan, dan haka suka buk'aci passport d'in baba k'arami da inna, ita inna babu, sai sunje an mata, amma baba k'arami an samu. Sun bari akan zuwa anjima za'azo akai inna tayo. Daga nan Galadima ya buk'aci number da aka kira aka sanar musu da accident d'in Abba. Daddy yace Ai'sha aka kira, saidai akawo wayar tata. Kiranta yay yace tabama cikin su Aryaan ya kawo wayarta. Babu dad'ewa saiga Aryaan d'in da ita, yanda yaron ya gaishesu saida abin ya birge Galadima, ya yarda yaran gidan akwai tarbiyya babu laifi kam. Galadima yace, “amma Dady ko numbers nawa Abba ke amfani dasu?”. baba k'arami ya bashi amsa da cewar “uku ne”. Nuren yace “kozamu samesu dukansu?”. Dukda baba k'arami da daddy sunshiga mamaki, dansu zukatansu basu kawo musu akwai wani Abu a k'asa ba, sun d'auka kawai Abba yayi Accident ne dai. Baba k'arami yabasu Numbers d'in duka. Bawani bincike Galadima yayi a wayar innarsu Munaya ba, wani Abu kawai ya saka (Wanda Nima ban saniba😱) yabama Dady wayar yana fad'in “zata bar wayar anan dan a can bazatayi aikiba, kuma gashi muna buk'atar wayar, dan haka daddy saika rik'e a hannunka tunda kai kana gida”. Dady ya amsa da to, duk su Galadima sun kuma sakasu a duhu. Sallama sukai musu suna fito domin tafiya. Harsun Shiga mota saiga Aiyaan da gud'u d'auke da wata Leda. Sarkin mota ya tareshi yana fad'in yaro miya farune?”. “Auntynmu za'a kaimawa inji innarmu”. Galadima yayma sarkin mota nuni da yabar Aiyaan d'in ya k'araso. Bud'e murfin Galadima yayi, Aiyaan ya k'arso, Galadima ya kamo hannun Aiyaan yana murmushi, “my friend ya akayi?”. 'Uncle innarmu ce tace akaima Auntynmu dan ALLAH”. murmushi Galadima yakumayi, sannan ya kar6i ledan yana fad'in “ita kad'ai banda ni?”. Aiyaan yad'an zaro ido waje, sai kuma yace “to bara naje Na fad'am innarmu kaima ta baka naka”. Da sauri Galadima ya kamo hannunsa dan yana neman tsillawa da gudune, “kaga dakata, idan naje saimu raba wannan da ita, yanzu dai ka fad'ama innarmu ta shiryaka gobe zan aiko a d'aukeka kazo ka zauna damu tunda kuna hutu ”. Cikin murna Aiyaan yace, “wajen auntymu?”. Galadima ya jinjina masa kai. “to amma kuma Aryaan fa?”. Cikin mamaki Galadima yace, “wanene Aryaan d'in?”. “lah baka San mu 2wins bane ba?”. “da gaske?”. “ALLAH kuwa”. “to shikenan, kacema innarmu ta shiryaku Ku duka biyun zakujema Aunty hutu”. Cikeda murna Aiyaan ya shek'a da gudu gida danya kai labari. Galadima yay murmushi yana rufe k'ofar motar, Nuren ma murmushi yakeyi, a fili yace, “yara sunyi wlhy”. Galadima ya kalleshi, cikin d'age gira sama yace, “kayi aure”. Sosai Nuren yay dariya. ****** A inda suka d'auki Nuren anan suka ajiyeshi, su kuma suka koma masarauta, sun iske tuni dogaran sun dawo abinsu. d'akinsa ya Shiga, ya iske Sauban nata barcinsa. Bai tadashiba, yadawo falo ya zauna. _____________________________ Da daddare Galadima Na falonsa zaune yana aiki a system akayi knocking d'in k'ofa, izinin shigowa ya bada, sarkin mota ya shigo hannunsa d'auke da leda. Galadima dake aikinsa bai d'agoba, a haka ya amsa gaisuwar sarkin mota. Sarkin mota yace “ranka ya dad'e kayi mantuwane a mota ”. d'agowa Galadima yayi ya kallesa, ganin ledar da Aiyaan ya kawo yatuna masa sak'on munaya, nuni yama sarkin mota daya ajiye. Sarkin mota ya ajiye yana masa saida safe. Nanma bai tankaba, kansa kawai ya jinjina masa. Bayan fitar sarkin mota ya mik'e d'auke da laptop d'insa da ledar, dama tunda ya shigo baima lek'a ta ba, dan Sauban yace yakai mata abinci, kuma tun d'azu suna tare suna hira. Hakan yasa yagane shine ta raina kenan. wannan haushin ya hanashi Neman inda take. A bakin gado ya isketa zaune tagama waya da Munubiya, k'in d'agowa tayi ta kallesa, tadai amsa masa sallama. Shima bai kula taba ya zauna bakin gadon d'an nesa da ita. Shiru kowa yayi suka share juna, haushi ya turnuk'e Galadima, lokaci yayi dazai daina d'agama yarinyar nan k'afa, yakamata su goga raini shi da ita. ta gefen ido ya saci kallonta, sai wani cika da batsewa takeyi, ya cije lips nashi. “k baki iya gaisuwa bane?”. Saida takuma tura bakin sannan tace “ina yini” tana mik'ewa da nufin bar masa d'akin, tana k'unk'uni Bai amsata, sai mik'ewa da yayi shima, matsawa tashiga yi baya yana binta, fuskarsa a matuk'ar d'aure, da jikin bango ta manne, shikuma ya mata runfa, hannunsa d'aya a dogare da bangon yayinda yasaka d'aya ya rik'o hannunta ya matsa da k'arfi, zatai magana ya jawota tafad'o jikinsa, ya manne bakinsa kan nata, duk yanda taso kwatar kanta hakan ya gagara, dan ya kama hannuwanta biyu ya murd'esu ta baya yanda ta kasa koda motsi. A haka ya wulk'itata takoma saman gadon, shima yabi bayanta. Ya d'ora hannunsa kan bakinta dan karta ishesa da tsiwa, idonsa ya saka cikin nata ya hanata kata6us, cikin tsare gida yace “dolene yau Na kora miki warning na musamman danki ringa banbance inda zakiyi tsiwa”. Bai bata damar dazata fad'i nata ba yashiga aikata yanda yakeso da ita🤥🙆🏻.................✍🏼 Kutttt Galadima auren Contract nefa😱😂, ba ruwana kaida masoyan Munaya aradu🤣⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀🤧. i miss you wujiga-wujiga my sweet fans😂😜😜😜🥳. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*🙏🏻😭 *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻9⃣ .................Salon nasa yasani bashi ragama, dan Galadima yazo min da sabon salo mai tafiya da gudun jini dana zuciya. Duk da kasancewata farin shiga, hakan bai hanani gane Galadima Na daban bane, kamar yanda kuka sanshi mutum mai izza da k'asaita, hakan bai canja ba ta wannan fanin, komansa a nurse da izzar k'asaita yake gudanar dashi. ban tashi farga nayi kuskure ba saida labari yafara nisan zango, anzo wajenda tsorosa yafara tasiri a gareni, Sai dai kuma nayi sakacin da Galadima yazama kurman dutsen dabaya ji baya gani. Sai lokacin hawaye suka fara ambaliya ga fuskata, hannayena na k'ok'arin d'agawa domin rok'o, sai dai ya hanani wannan damar gaba d'aya.......... 🤥🙆🏻kai babu ruwana, iya nan nagani nima🤫 aradu aunty Magajiya da aunty Ni'ima zasuci k'aniyata ne idan na k'arasa fad'a😱🤭⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Tabbas na gurzu, dan yau na banbance tsakanin aya da tsakkuwa, banbancin baya cikin hayyacinsa da yau d'inma kad'anne, dukda babu yanda za'ayi daren farko yayi dai-dai da kowacce rana ta bayansa. Duk ajiyar zuciyar danake saukewa yana jina, amma yay luf a gefena, hakan ne Yakuma tunzurani, a zalinceka akasa lallashinka saboda jin kai, wlhy kasaitar bawannan tayi masa yawa, duk randa yazama sarki kam fadawa sunga takansu, dan magana dai idan sarki na uku a fada toshi bazaiyi ko guda d'aya ba😏. Galadima daduk yake sauraren kukan nata da ajiyar zuciya ya juyo kad'an yana fuskantarta, hannu yasaka ya tallafo fuskarta ta matso dai-dai da tasa, jinai kawai ana huramin iska saman ido, tsaf na fahimmci iskar bakinsa yake huramin, amma saina dake nak'i bud'e idona. Muryarsa can k'asan mak'oshi ya furta “my friend are you okay?”. Banza na masa, nakuma k'i bud'e odon, lallai mutuminnan yacika d'an latsin rainin wayo number 1, yanzunan Galadima har yanada bakin yimin wannan banzar tambayar?, idona a rufe har yanzu na bud'e baki cikin salon tsiwa zan maka masa bak'ar magana, amma saiya d'ora yatsansa saman bakina yana fad'in “shiiii!🤫” da bakinsa, shirun kuwa nayi kamar an rufemin bakin Dan Nina Na tuna illar yin tsiwar.(😝😂) Ya matso dani jikinsa ya rungume, hannunsa na buga gadon bayana k'ad'an-k'ad'an, ya d'ora bakinsa saitin kunnena, “yanzu kin gane banbancin Sameer da Munaya right?, idan kuma har yanzu baki fahimta ba to bakinki ya cigaba d'amin tsiwa OK?, nikuma bazan gaji da punishment nashi ba sala-sala yalla6iya💋”. ‘ya k'are maganar da sumbatar cikin kunnena’. Babu shiri na k'ank'amesa dan har cikin kwalwar kaina naji sumbar nan. Kad'an ya buga bayana sannan ya janyeni daga jikinsa ya sauka daga saman gadon. “hasbinallahu wani'imal wakil” na iya maimaitawa kawai, na k'ank'ame pillows d'in gabana ina rintse idanu da cije lips (copy copy😝). Kusan mintuna 15 duk nazata yama fitane, sai kawai jinai an d'aukeni. a razane na bud'e idanuna, kallon ido cikin ido mukaima juna, da matuk'ar Sauri na maida nawa na lumshe. Wani muskilin murmushi Galadima yayi yana cije lips. Ba shiri na bud'e ido, saboda jina cikin ruwan zafi, yunk'urawa nayi zan mik'e cikin 6ata fuska ya maidani ya zaunar yana fad'in “za6i ya rage naki, zama kiyi da kanki, kokuma ni nayi miki..” Banma bari yakai k'arsheba na koma na zauna ina kare k'urjina. Kafad'a ya d'age sama yana ta6e baki da fad'in “hummm”. Fita yay daga bathroom d'in ya rufe mata K'ofar. Na kai tsawon lokaci a bayin ina Gasa jikina, dan nasan idanma banyiba kaina nama mugunta, saida naji ko ina ya saki sannan nayi wankan tsarki ina hawaye, bansan yanda zan fassara wannan muguntar ta Galadima ba kuma, wannan karon kuma tsautsayin zaice kokuwa ba yin Kansa bane?. Haka dai na kammala na d'aura towel d'ina, a zuciyata ina addu'ar ALLAH dai yasa ya fita, dan towel d'in guntune, bai gama rufe cinyoyina bama baki d'aya. Da sand'a na fito, yauma inajin zafi kad'an-kad'an, amma ba kamar na ranar ba. ganin baya d'akin saina ida rufe k'ofar na tako cikin d'akin sosai. Ina neman kaya a wardrobe ina share hawaye, indai rashin tsiwar dayake fad'ace na daina masa, dan bazan zauna ya illatani a banza ba, wannan k'addararren cikinma daya hanamin gangar jiki hutawa da ciwuka ya isheni, basai na cigaba da 6alloma kaina wata muguntar tasa ba. wata 'yar riga mai d'an nauyi-nauyi na samo, na cirota dan sanyi nakeji, juyowar da zanyi saina gansa zaune bakin gado yana danna laptop, hannunsa d'aya rik'e da glass cup yana shan fresh milk hankali kwance. Saida nad'anja baya, nakuma bud'e rigar ina kare jikina. Duk abinda takeyi yana kallonta ta gefen ido, amma yawani share kamar baima San da itaba. Da bin bango da sand'a na koma bayin, ta gaba kuma ina karewa da rigar. Saida ta shige ya d'ago kai yana kallon k'ofar bayin, saikuma ya girgiza kai yana murmushin gefen baki. cigaba yayi da aikinsa a nutse. Barci nakeji, ga zazza6i yafara rufeni, hakan yasa ina gama saka rigar na fito, naci serious kawai sannan na fito. d'ago idanu yayi muka had'a ido, da sauri nad'an rankwafa inajan rigar barcin k'asa wai danta rufemin cinya zuwa kwauri. Baki ya ta6e yana wani janye ido cikeda basarwa. Irin shi baiga abin kallo d'in nanba. Ni kuma na dalla masa Harara ina k'ok'arin hayewa gadon. “ji mana”. ‘yafad'a cikin izza’. Banza na masa zan haye gadon. Yace “iyim, bakije daddarawa ba kenan yarinya, saina sake kaiki yanzunnan....”. Kafin ya rufe baki nama iso gabansa na tsaya. d'agowa yayi yana kallona yana kur6ar fresh milk nashi, ya d'agamin gira d'aya. Baki na turo masa ina share hawaye. Ya kamo hannuna ya zaunar kusa da shi, “nikam yalla6iya karki haifomin abin cikin kwan da halin kuka, bana son ragwan taka, 'yata ko macece jaruma za'ayi, irin wadda labarinta zai zaga lungu da sak'o na duniya”. Harara na balla masa, yay saurin rik'e cup d'in hannunsa dayake zuba frash milk a ciki, “eh me, malama karkisa hantar cikina fitowa, irin wannan harara haka”. Kad'an yarage banyi dariya ba, da gaskiyar Momma, halin Galadima d'aya da Sauban, tsantsar harmutsine da sanya damuwa a rai ya lullu6e halinsa na barkwanci, hakan kuma yanada nasaba da rashin samun mai jansa a jiki yana d'auke masa kewa da rage masa rad'ad'in damuwarsa. Momma hankalinta nakan jiyyar Abie, Aunty mimi kuma rainon Sauban, mom kuma tayi aure lokacin dayake buk'atar makusanci, s....... Firgigit nayi saboda hancina da yaja, na kalleshi ina tura baki. “maida wuk'ar yalla6iya, abin bana fusata bane, wace duniyar kika tafi hakane da nisa inata magana?”. Marairaice fuska nayi ina shirin fara kuka, “please ka barni na kwanta barci nakeji”. Kofin hannunsa ya mik'amin, na waro idanu ina girgiza masa hannu alamar a'a”. Shima saiya waro nasa idanun yana fad'in “why?”. “kawai ni bazan sha bane, aje a zubamin wani abu”. “hakane kuma”. ‘ya fad'am yana kamoni ya jawoni jikinsa’. Saman cinyarsa na zauna, da hanzari nafara k'ok'arin mik'ewa. shima saiya kama hannayena ya maidasu baya yanda bazan iya kata6us ba, madarar ya d'auka ya guntsa da yawa a bakinsa. Waro idanu nayi ganin ya nufo bakina gadan-gadan, duk yanda naso kauda fuskata ya gagara, na datse hakwarana da sauri, shi kuma saya toshemin hanci, hakan yasa ni bud'e baki dole, dan ina buk'atar shak'ar numfashi. Tas ya juyemin fresh milk d'in abakina, sannan ya kuma rufe hancina saida na shanyeta sannan ya janye bakin, ni dashi duk muka hau sauke numfashi, kuka na sanya masa, amma hakan bai hanashi kuma guntsar madarba ya kuma juyemin a baki na, haka yayta min, ya kuma k'ara rabin kofi kuma, saida yaga ta kwalin ta k'are sannan ya sakarmin hannu na tashi zaune. Bansan kawai na fara kaima k'urjinsa k'ananun dukaba, ina fad'in wlhy sai ALLAH ya sakamin, kai bama zan yarda ba fa, saboda k'azanta kaita had'a yawunka da fresh milk kana d'uramin, ni bazan yardaba”. Shagala kawai yayi yana kallona, yakasa kare kanshi balle yunk'urin hanani, saida nayi mai isata sannan na fad'a k'irjin nasa ina raira kuka. Lumshe idanunsa yayi yasaka hannayemsa ya zagayeni sosai yana kuma sakani jikinsa sosai. Nima sainayi luf Ina shak'ar k'amshinsa da yariga ya mannema fatarsa. Munja wasu times a haka, ni ina kuka shi kuma idonsa a lumshe yana shafa kaina da saurarena. Jiyay kawai jikinta ya saki, alamar barci ya d'auketa, sai ajiyar zuciya da take ta saukewa, bud'e idonsa yayi, sannan yakai bakinsa a hankali ya sumbaci sumar kanta dake tare da danshin ruwa har yanzu. zafin zazza6inta dake ratsa 6argon jikinsa ya sakashi fidda huci yana kuma sumbatar kanta. Dr Farida ta sanar masa babu abinda zai hanata wannan zazza6in, koda tasha magani ya sauka saiya dawo, sai idan cikin yayi kwarine maybe ta daina ma gaba d'aya, amma mai juna biyu ba'a rabata da k'ananun ciwo makamantan haka. jiyay ya kuma k'aunar Momma d'insa a ransa, a hankali ya furta I love you my Momma”. Tashi yay d'auke da Munaya a hannu, ya kwantar da ita sannan yaja bargo ya lullu6a mata. tare da sunkuya wa ya sumbaci goshinta ya shafa cikinta da hannunsa sannan ya mik'e ya koma inda yake. Ya cigaba da aikin dayake a laptop Wanda ban fahimci komaiba a ciki, tsawon lokacin yana aikin, saida ya fara hamma sannan ya kashe. bayi ya shiga ya d'auro alwala, ya gabatar da nafila kafin yay shafa'i da wutiri yaja doguwar addu'a da kirari wa Ubangijin talikai, harda hawayensa sannan ya mik'e. Ya kuma daidaita hasken fitilar d'akin sannan ya hau gadon shima ya kwanta, yay musu addu'a ya shafe cikin munaya (😂Galadima saboda tsaro ba tsoroba ko🥺). a zatona zai rungumeta, sai naga ya gyara kwanciyarsa kawai a gefenta yaja bargo shima. Galadima asuba ta gari, (ni dai rungume nawa mijin zanyi aradu🤫🙈⛹🏻‍♀). Ga bannin asubahi zazza6in munaya ya sauka, hakanne ya sakata samun dad'in barci sosai, ta kuma kanainaye Galadima, wanda shi da kansa ya mirgino har inda take cikin barci ya rungumeta, dukda zafin zazza6inta nata ratsa nashi jikin yakasa barinta. ahaka kiran sallar farko ya riski kunnuwansu. Kusan a tare suka farka, ganinsu manne da juna yasaka kowa barin jikin d'an uwansa da sauri, munaya dai kunya ta sakata juya baya, amma boss ko a kwalar rigarsa, saima tashi da yayi yana wani ciccin Magani ya shiga toilet. Alwala ya yo, baiyi mata magana ba ya fice abinsa. Munaya ta raka bayansa da harara tana fad'in Girman kai dai rawanin tsiya wlhy. tashi tayi itama ta shiga bayin, amma sa6anin shi ita harda wankan gasa jiki (lallai kinji basawa Munaya🤭, wannan gasa jiki dabaya k'arewa haka🤥😂). Fitowa tayi tanata kumbura fuska, ni dai na lalla6a na shige bayinta danna dandalo arzik'i😝 lol (koya kukace fans🤷🏻‍♀😂?). **************************** Ban sake jin d'uriyarsa ba sai around 9:30am. Tashina a barci kenan na rarrafa zuwa bayi da k'yar nayo wanka, dan banajin dad'in jikina gaba d'aya, danan ya saki sai nan ya kama ciwo. Motsin mutum naji a bayana dan haka na waiga, Galadima ne cikin Farin wando da t-shirt itam fara tas, ya d'aure k'ungunsa da Navy blue d'in belt, sannan ya kawo jacket navy blue itama ya saka, babu takalma a k'afarsa, sai dai k'afar fes tamkar ba'a takata a k'asa, sai agogon azurfa mai k'yau d'aure a tsintsiyar hannunsa. hummm dan k'yau kam dai yayishi, sai dai ni bawai ya birgeni bane😏 (ho Munaya banda zuk'i ta malli dai🤥🤣😝🙆🏻). Janye idona nayi na maida kan gyaran gashina da nakeyi. Shima baice uffanba ya wuce wajen frigate, fresh milk ya d'akko yatako gaban mirror inda nake zaune. a saman mirror ya ajiye kwalin madarar ya jingina bayansa shima, idonsa a kan gashina danake gyarawa. ya d'au madarar ya zuba a cup d'in daya d'akko tare da mik'omin. “ni ba ita zan shaba”. na fad'a ba tare da na kalleshi ba. “mikenan?”. shima yafad'a cikeda k'asaita. Yanzunma ban kalleshi ba nace “tea”. Kofin ya dire saman mirror yana tattare hannun rigarsa, “salon ki k'onamin idon abin cikin kwan kenan, to za6i ya rage naki, sha da arzik'i ko kuma d'ura”. Babu shiri na d'auki kofin na kwankwad'e, dama iyayine inajin yunwar. Kofin na mik'a masa ina 6ata fuska tamkar zan fasa ihu. Ya d'agamin gira yana fad'in “taimakon kai my friend”. Gefe nayi da fuskata ina fad'in “kai duk salon mugunta ka sani ai”. “martabar gudan jinina nake karewa”. yay maganar yana k'ok'arin ficewa. Baki na na ta6e ina harar bayansa, su gudan jini anji jiki kuwa. Ganin zai fice nai saurin cewa “nifa inason zuwa kitso, kuma zan koma school”.. Tsayawa yay cak daga yunk'urin fitar da yakeyi, Batare daya juyoba yace “babu wannan tsarin a masarautar gagara badau”. Yana gama fad'a ya ida ficewarsa. Tamkar zan fasa kuka nayi jifa da cumb d'in hannu na ina fad'in “ina ruwana dawani tsarinku ni, makaranta ta nakeson komawa ehe”. Yana jiyota amma ko'a jikinsa yaci gaba da k'ok'arin fitarsa hankali kwance. ★★★★★★★★★ Tunda Aryaan ya shigo da gudu inna ta tareshi tana fad'in “kai lafiya? minene na gudu?”. “innarmu wlhy Uncle ne yace ki shirya mana kayanmu ni da Aiyaan zai aiko gobe a kaimu wajen Auntynmu”. Inna tayi d'an murmushi kawai, dan ita bata d'auki maganarma serious ba. Su dai su Aiyaan sunata murnarsu, sun tafi d'aki sun hau had'a kaya. Babu dad'ewa da yin haka saiga daddy ya shigo da sallama, inna ta amsa masa tana gyara zama, shima zama yay kujerar dake kusada k'ofa, ganin haka inna ta fahimci da magana yazo, dan haka ta maida dukkan hankalinta Kansa. Bayani yamata dalla-dalla akan zancen da su Galadima sukazo dashi, ya d'ora da fad'in “saiki shirya dan zamuje ai miki passport”. Inna tace, “amma dadynsu nake ganin ai da kud'in kukaje kamar zaifi”. Murmushi Dady yayi, yace “Ai'sha nasan miyasa kikeso zamewa, to ai kaf cikin matan yayan kece ya cancanta kije koda ace bawai Galadima ne ya biyaba, maganar ciwo Muke bawai jin dad'i ko gutsiri tsomar wasu ba, ki shirya dan zai turo wanda zamuje immigration office d'in”. daga haka ya tashi ya fice. Shiru kawai inna tayi, itadai inda ta itace da antafi da ko innaro, dan tasan wannan tafiyar dukda ta ciwoce sai ta janyo 6acin rai a gidan. Aiko tamkar inna tasani, dan ana fad'ama innaro tace “bata amince ba, ita ta haifi auwalu kuma da ita za'aje tayi jiyyar yaronta, bazata bama kowacce mace acikinsu wannan ragamarba. Shiru baba k'arami da daddy sukayi, taci masifarta ta gama tayi shiru. Baba k'arami yace, “amma dai inna kinsan jinyar Yaya sai da matarsa a kusa, kekuma k'arfinki ya k'are ya za'a d'ora miki d'awainiyar da matansa ne keda hakki a kai?”.. “yo d'awainiya ba tare da kai za'a tafiba? Kai basai kamasa ba. ni dai fa ban amince Ai'sha tajeba, dan wlhy bazan ta6a son Ai'sha ba komi zata zama, tunda dai ta silar jikokinane balle amin ilimi. k'ilama itace ta jefeshi dan taga ta kama k'asa 'yarta Na auren d'an Sarki, t........”. “innaaaa! haba mana, dan ALLAH karma ki bari maganar nan ta fita, waishin minene laifin Ai'sha a gareki? duk cikin matanmu banga wadda take girmamaki da d'aukarki matsayin uwaba irinta, inna ya kamata wannan k'iyayyar ta koma soyayya hakanan, a baya kince dan basuda asali, kin dawo kince juya ce bata haihuwa, gashi kuma yanzu har ALLAH zai fidda jikoki daga tsatsonta, to miye kuma matsalar?”. “toko zaka shak'eni Na fad'a makane Hameesu?”. “a'a inna, ALLAH yabaki hak'uri”. “kaidai ka Sani, ni yanzu bara Na tashi Na shirya Ku kaini inama kace, imagesa nema ko uwarmi oho”. Daga Dady har baba k'arami babu Wanda ya tanka mata, tana shigewa baba k'arami ya mik'e yana cema dady “yaya ka jireta, bara naje mutafi da maman 'yan biyun, kota fito kace naje shiryawa ne”. Kai Dady ya kad'a masa yana murmushi, baba k'arami ya fita da hanzari. Bayan wasu mintuna saiga innaro an fito ana warware gyale za'a yafa, “yauwa jafaru muje Na shirya”. Habiba dake kitchen tana girki duk diramar da ake tana saurare ta tuntsure da dariya, lallai tsohuwarnan akwai daru, mama Na hanya ai, itace maganinki (gwaggo Safiyya mamarsu). Kallonta Dady yay yana murmushi, yace “to inna mu jira jafar d'in yaje shiryawa”. “ato shikenan bara kafin ya dawo nad'anci abinci, k! Habiba zubomin idan abincin nan ya tsotse, gara Na fita cikina da d'an nauyi”. Habiba ta had'iye dariyarta sannan tace “innaro bai tsotseba, amma nanda kamar dai minti 5”. “babu damuwa ai, nasan jafaru ma bai dawoba harnaci, kinsan shi da dak'undar shiri, ya tsufa amma kullum kallon kansa yake sa'ar Abdul-hameedu”. Dariya Dady ya had'iye da k'yar, yasa handkerchief yana toshe baki dan karta fito. ★★★★★★★★ Tsaf na kammala shiryawa sannan Na kimtsa d'akin, ni dukfa a nufina nayi shirin asibitine. Fitowa nayi dan naga ko yana falone, wayam babu kowa, sai sallama da nakeji a bakin k'ofar, amasawa nayi na bada izinin shigowa saboda naji muryar matane. Su 10 ciff suka shigo, k'asa suka zube suna gaisheni, Na amsa musu da 'yar sakewa, “lafiya dai?”. “lafiya lau ranki ya dad'e, mune zamu kasance hadimanki, masu miki dukkan hidima. Nifa wlhy banason wasu bayi, amma dolene Na barsu tunda wad'ancanma Galadima ne yace su tafi, yanzu kuma baya wajen, ni kuma banida ikon korarsu tinda bansan kan abinba. Amsa musu nayi da “to” sannan nawuce Na zauna a kujera. Tasowa sukai suka biyoni, a tsanake suka dinga fad'amin sunansu da aiyukan da zasuyi. Wad'anda naga bazan iya yarda suyiba Na canja musu aiki. Sallamarsu nayi, Ina k'ok'arin tashi Na shige ciki saiga Sauban ya shigo, duk zubewa sukayi suna kwasar gaisuwa a gareshi, ya amsa musu yana wani yatsine face, sai kuma ya basu izinin tafiya, fita sukayi harabar sashenmu. Na kalleshi ina murmushi, “ashe kaima dai sarautar Na jininka yaa Sauban? Wanda bai saniba saiya d'auka duk bazaka iya wani Abu daya shafi sarautaba”. Dariya yayi yana zama, “aunty gimbiyar mu kenan, wannan ai sai mijinki”. Nima murmushi nayi kawai. Ya mik'omin kayan hannunsa yana fad'in “ga break fast d'inki”.. “wayyo yaa Sauban, nikam dai nagaji da ciye-ciyennan ma, zuwa zanyi Na fara abinci da kaina”. “wlhy dakin taimakemu Aunty gimbiya, mijinki shiya saba da cin abincin waje shiyyasa bai damu ba, ya kamata kafin Na wuce gobe naci girkinki”. “kamarya gobe? Kana nufin zaka koma kenan?”. “tab da gudu kuwa, aini bazan iya zaman k'asarnanba Na tsawon lokaci, tarema zamu wuce da Abba ai, harma da innarmu, yaa Sam bai sanar dakeba kenan?”. Baki bud'e Na girgiza masa kai alamar a'a. Sauban yay murmushi, “kinsan halin Galadiman namu ai, soyake yamiki surprise maybe, yanzu hakane yaje cuku-cukun visa d'insu ne. waito miyasa bazamu koma tare da kubane?”. Murmushin yak'e nayi, nace, “maybe akwai ayyukan dabai gamaba shiyyasa”. “inaga hakanne kam, ni bara naje, yace Na iskeshi birnin gayu, ga mahfuz can Na jirana”. “ok sai kun dawo” Na iya cewa, danni daga 'yan matan masarautar har samari ba kowa Na saniba, tunda time d'in daya kamata nad'an San mutane sai muka tafi India. ni bama nason Na saba da kowa, ni da ba zama ya kawoni ba. Maganar fita da Abba da Galadima yakeyi sai yayta cin zuciyata, kimar Galadima da darajarsa saita cika zuciyata, inason mahaifana, kuma dukkan Wanda zai nuna musu kulawa bazan manta da shiba, harda 'Yar kwallata Na share, Na tashi Na koma bedroom ba tare da nayi break fast d'inba ma. ***************************** Innaro dai tun ana jiran dawowar baba k'arami harta fara gyangyad'i, habiba data kammala abincin ta d'ebo ta kawo mata, nuni Dady yay mata akan ta koma. Habiba ta koma da baya ba tare da ta k'araso falonba. Tun tana gyangyad'i harta 6ingire a kujerar barci mai nauyi ya d'auketa (ho innaronmu ta mutunci🤸🏻‍♀😜). Baba k'arami da innarsu munaya kam tuni sunyi ficewarsu, dayake Abu Na kud'i dandanan aka gama cuku-cukun komai, Nuren ne tsaye, saida komai ya daidaita suka samu visa d'insu a hannu sannan suka fito. Har gida ya maidosu ya koma suna jera masa godiya da addu'a shi da Galadima. Innaro daga gyangyad'in jiran abinci ya tsotse aka zarce da barci mai nauyi, shima Dady lalla6awa yay ya fito dan asibiti zaije. Tafiyarsa babu dad'ewa saiga gwaggo Safiyya ta iso da yaranta biyu. Hayaniyar su Dahiru ita ta tada innaro, ta mik'e zumbur tana fad'in “yauwa Jafaru kadawo mu tafi ko? Habiba bar abincin kawai idan muka dawo naci. Mi Dahiru da Naja'atu zasu ba dariya ba, suka shiga shek'ama innaro dariyar shak'iyanci. Wai kota kwanta da yunwa ne. Zaginsu ta hau yi ta d'auki filon kujera tana dukansu. Sai da gwaggo Safiyya ta musu magana sannan suka nutsu, “inna ina zakuje da Jafaru ne?”. Gyara zama innaro tayi tashiga bama gwaggo Safiyya labari. Murmushi kawai gwaggo Safiyya tayi, danta gane wayo suka mata suka gudu kawai, itama sai tace “to inna ki cigaba da jiransu, k'ila dan sunga kina barcine suka jira ki tashi sannan Ku tafi. Da wannan gwaggo Safiyya ta rufe bakin innaro ta zauna jiran su dady. Aiki🤣🤣😝. ********** Galadima daya fita kai tsaye asibiti ya nufa, su yaa hameed kawai ya iske can, dan dady ya hana matan gidan zuwa sai anjima, doctors Na complain akan suna cika wajen da yawa. Cikin mutunta juna Galadima ya gaisa dasu yaa sabi'u sannan yashiga yaga daddy. Yau kam Alhmdllh dan ba barci yakeba, kumbirin fuskarsa kuma yad'an sa6e kad'an, saidai baya iya magana sai dai yayta bin mutane da idanu. Dukda bazai iya amsawa ba haka Galadima ya risinna ya gaidashi, tare da masa fatan samun lafiya sannan ya fita office d'in doctor. Bayan sun gaisa doctor ya bama Galadima file d'in bayanan Abba dasuka tattara. Kar6a Galadima yayi ya duba, dukda bawai ya fahimci bayanan bane, ( kusan dai rubutun doctors sai su). Suka d'an tattauna akan cigaban da aka samu sannan Galadima ya fito. Ya iske daddy ya iso, suka gaisa sannan yamasa dukkan bayanan da doctor yamasa shima. Dady ma yaji dad'in cigaban da aka samu. Galadima yay musu sallama ya fito. Guntun tsaki yaja saboda yanda jama'a suka wani zuba masa idanu tamkar sunga magiji, da sauri wani dogari ya bud'e masa motar ya shiga, sannan suma suka shiga. Daga asibiti Galadima yace su wuce birnin gayu plaza. Cike da girmamawa sarkin mita ya amsa da to. Maida kansa yayi jikin seat ya kwanta tareda lumshe idanu ya fad'a duniyar tunani................✍🏼 Barkanku da juma'a💋💋💋🤝🏻. Musha weekend lafiya sisters⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀😄. *_ALLAH ka gafartama iyayen mu_*🙏🏻😭 *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 _________________________ _Duk marubucin daya kafa alk'alaminsa bisa takarda tabbas yagama tanadar yanda labarinsa zai kasance ne, amma sai wasu wabubuwan mamaki kaga sun gaza k'arewa a social Media, ban saniba ko samunmu available ne yakesa a kullum kuke mana kallon marasa aikinyi?, ni dai nasan time d'in dana shirya labarin RAINA KAMA ban zauna tebirin shawara da kowaba a online, inkuwa hakane tayaya wasu har suke tunanin nafara sauka akan layin labarin?, to magana d'aya zanyi a wannan ga6ar, ban gina labarin Raina kama akan kwanciyar aure bane, dan haka masu maganar munaya bata da aiki saima Galadima rashin kunya saisu jira saina kai k'arshen labarin kafin su k'alubalanceni, abin dariya, (wai aikina kenan daga nasa munaya ta murgud'a baki sai ta harari Galadima da masa k'unk'uni) tunda aikina kenan babu lallai wajen 6ata lokaci karantawa, haka Na tsara labarina tun farko kuma haka zanyi, duk wanda yaga bai masaba zai fara iya rubuta nashi shima kawai. wannan abun da kukema writer's yana 6ata mana rai, bai kamata ku dinga k'alubalantar writer's ba, bayan su suke da masaniyar yanda suka shirya labaransu, idanma zakuyi saiku ringa tanadar lokaci har zuwa bayan mun kammala, hakan zaifi tasiri fiyeda katsalandan a tsakkiyar labaran mu, akoda yaushe kuzama masu kula kafin Ku k'alubalanci mutum🤷🏻‍♀._ *Ba akan kaina kawai nayi wannan bayaninba, harda sauran writers da yawa da akema makamancin hakan koma fiye da nawa.🙅🏻* _____________________________ ~Book 2~ 👉🏻1⃣0⃣➖1⃣1⃣ ...................Koda motocin suka tsaya sarkin mota ya bud'e masa k'ofa yakai tsawon lokaci baiko motsaba, saboda tsantsar tunani da zuciyarsa ta lula, aduk sanda zuciya take cikin matsanancin matsi gangar jiki ma gazawar karfin ikon jini dana 6argo sukan mata k'aranci, shi kansa yasan yanada buk'atar mataimaki a kan wannan lamarin, amma k'arancin rik'on amana Na d'an Adam ne yake yawan gargad'arsa da taka masa birki, ba kowane zai fahimci ma'anar nok'ewar tasaba, sai mutum daya tsinci kansa a makamancin halin da yake ciki......... “Ranka ya dad'e mun iso”. Sarkin mota yasake fad'a cikin taraddadi da taka tsantsan. A hankali Galadima ya bud'e idanunsa da suka koma launin jaa saboda damuwa a kan sarkin mota, batareda yace uffanba ya ziro k'afarsa k'asa yana cije lips da had'iye wani kududun damuwa a mak'oshi. Tunda ya fito ma'aikatan wajen suketa masa sannu da zuwa, dan tunda ya shigo k'asar sai yanzu ne zai shiga cikin plaza d'in. Hannu kawai yake iya d'aga musu, amma bakinsa yay masa nauyi, kallo d'aya kuma zaka masa ka nazarci damuwa da buk'atar hutun dake tartare da kuzarinsa. A cikin plaza d'in ma bata sauyaba, d'aga hannu agaresu shine yazama linzamin amsa gaisuwar dasuke masa. Da hannu yayma d'aya daga dogaransa nuni da amso masa key. Da sauri dogarin ya amsa yana mai nufar sashen da zai kaishi office d'in Saleem mai kula da CCTV camera's. Sai dai kafinma yakai ga k'arasawar suka had'u da saleem, Wanda tun shigowar motocin Galadima ya gansa. Keys d'in ya damk'ama dogarin, sannan ya k'araso domin mik'a gaisuwa ga ogansa na wajen aiki kuma magajin garinsa. Shima d'in dai hannu Galadima ya d'aga masa, hakan kuma ya saka Saleem fahimtar akwai damuwa kenan. Koda aka bud'e ya shiga saiyayma dogaransa nuni da suje kawai, sannan ya maida idanunsa ya lumshe tareda kwanciya jikin kujerar yana lilawa a hankali. Shi kansa baisan tsawon lokacin daya d'auka a hakanba, amma tabbas yasan yashiga kudin nazari mai zurfin gaske. Knocking d'in k'ofar da akayi yasakashi bud'ar baki da k'yar ya bada izin a shigo. Nuren daya shigo ya maida k'ofar ya kulle, kafin ya ida takowa cikin office d'in, idonsa nakan d'an uwannasa. Zama yay a d'aya daga kujerun dake fuskantar Galadima, “brother what happen?”. “Northing”. Galadima ya fad'a batare da ya bud'e idonsa ba. Shiru kawai Nuren yayi shima, ya d'akko laptop a briefcase d'in daya shigo da ita, kunnawa yay, kusan mintuna biyu ya d'ago ya kalli Galadima, sai kuma ya maida kansa ga laptop d'in. “Sameer nasan kaga cigiyar da akeyi takowacce kafar yad'a labarai ta k'asarnan akan d'iyar minister, sannan jami'an tsaro tsaye suke akan binciken inda take. yakamata musan abinyi kafin lokaci ya k'ure mana”. Guntun murmushi Galadima yayi, batareda ya bud'e idanunsa ba yace “Nuren indai har babu wata waya datake aiki inda kakai yarinyarnan, kuma ka cire sim card d'in phone nata a lokacin daka d'auketa, to babu wata hanya dawani jami'in tsaro zai ganota, dama hanya d'ayace da kuskure zai basu damar bibiyarta, na d'aya lokacin daka d'auketa yazam wayarta na aiki, tabbas zasubi ta wannan hanyar su gano har iya inda ka kashe wayar, hanya ta biyu itace ka kashe wayarta baka cire sim card d'in ta ba daga phone nata, koda wayar a kashe take zasu bibiyeta ta hanyar 📡 su ganota” ya tashi zaune sosai yana bud'e idanunsa akan Nuren, “wannan hanyoyin biyu kawai ke garesu saikuma idan da camera tare da ita, idan duk babu wannan basuda wata hanya, ka kwantar da hankalinka my brother, komaina da tsarinsa right?”. Murmushi Nuren yayi, kafin ya salute d'in Galadima yana fad'in “I thrust to you my dear broth”. Shima galadima salute d'in Nuren d'in yayi yana murmushi. Komawa yay ya sake kwanciya jikin kujerar, “yanzu inaga time d'in turama minister Massage yayi?”. Cikin zaro idanu Nuren yace “baka kallon hakan a matsayin ganganci kuwa?”. Baki Galadima yad'an ta6e yana crossing k'afarsa, cikeda izzarsa yace “sai idan nabama wani damar hakan ai”. Nuren baice komaiba, dan yagama sanin hatsabibancin Galadima wajen iya sarrafa Computer, dan haka ya bar wannan zancen ya d'akko wani. “yauwa to maganar Malam Saminu fa? Kasan yana hannunmu fa har yanzu?”. “wannan barsa saiya kuma magantuwa, dan da alama yasan wani Abu, saidai akwai abinda ya sakashi za6ar 6oyewa. ni yanzu damuwar 6atan Muftahu yafi damuna, nasaka camera's jikin mutane 10 danake iya zargi a masarauta amma banga alamun da hannun koda mutum d'aya ba, hakan ya tabbatar min da gaske Muftahu na bibiyar lamarina, sai dai bansan dalilinsa ba, ko kuma waye sakashi?”. Nuren ya jinjina kansa, “brother aini da Harun dama mun dad'e da zargin Muftahu, Kaine kawai kake masa kallon mutumin kirki daman”. Lips kawai Galadima ya cije, amma baice uffanba, Nuren yaci gaba da 'yan danne dannensa a laptop d'in, zuwa wasu mintuna batareda ya d'agoba yace, “maganar Sirikinka fa?”. Shiru Galadima ya masa, saida ya mula dan kansa sannan ya murmusa tareda maida idonsa ya lumshe, “a daren jiya nagama da wannan matsalar, sim card d'insa 3, akwai Contact 300 da 38, mtn yanada mutum 172, ya fara saka credit a layin shekaru 15 kenan, ranar 3/6/2005, glo 107, ya fara amfani dashi shekaru 8 kenan, wad'annan sune Sim card d'insa da yake mu'amulla da kowa a ciki, kuma anfi saninsa da su, akwai 6oyayyen layinsa Na mtn shima, yafara aiki dashi shekaru 13 kenan, kuma mutane 59 ne kawai acikinsa, sannan ba kowane yasan layinba, dan dukkan family nashi basu San da zamansa ba, ita kanta mahaifiyar su Munaya batasan anyi saving number a phone nata ba, suma da suka kirata basusan da number a wayarta ba, dan baita6a kiranta da shiba, akwai matakan tsaro dake tattare da Layin, hakanne ya tabbatar min da akwai abinda yake 6oyewa a Sim card d'in, dan sai time to time yake amfani da shi, kiran matarsa da sukayi da layin wannan shine kuskuren farko da suka tafka da Sameer ya samu hanyar musu takun sauro. zan fara aiki akan layin na shigesu ta hanyar da basu zataba”. Jinjina kai kawai Nuren yakeyi dan mamaki, Galadima da banne, kamar yanda basirarsa take daban, ya sauke ajiyar zuciya yana kama hannun Galadima da idonsa ke a lumshe har yanzun, cikin karsashi yace “lallai kai RAINA KAMA ne Sameer”. Murmushi kawai Galadima yayi, amma baice uffanba. Knocking akayi, Nuren ya kalli k'ofar yana bada izinin a shigo, Sauban ya shigo da sallama, su duka idonsu a kansa, Nuren yace “lafiya kuwa?”. Zama Sauban yayi yana sauke Numfashi da k'yar, cikin magana d'ai-d'ai da alamar a birkice yake yace, “wlhy Yaya binmu aka ringayi da wata bak'ar Jeep, da k'yar mukasha wlhy, ni dai yau zanbar k'asarnan gaskiya”. Sauban ya fad'a tamkar zaiyi kuka’. Gani kawai sukai Galadima yana dariya, saida yayi mai isarsa sannan ya tsagaita. Nuren da Sauban suka tsaya kawai suna kallonsa. Tashi yayi tsaye yana takawa cikin izzar k'asaita, ya dafa bango yana lek'en waje ta window d'in office d'in, yakai wasu adadin lokuta a wajen, sai kuma ya juyo yana kallon Nuren d'in da Sauban da suma suka zuba masa idanu. “my dear brother! daka tsaya sun kamaka ai, tabbas da wannan shine kuskuren da zasuyi Wanda bazasu ta6a mantawa da waye Muhammad Sameer Saifudden ba a tarihin rayuwarsu. Waya gaya maka kana yawo cikin 9ja ne batareda idon Sameer ba a kanka?”. Sauban ya sauke ajiyar zuciya yana share gumin daya jik'a fuskarsa, “wlhy yaa Sam daka fad'amin da bazan tsorata ba”. Daga Galadima har Nuren dariya suka kwashe da shi, Nuren ya dafa kafad'ar Sauban yana fad'in “matsoracin banza”. “uhm-uhm yaa Nuren bazaka ganeba wlhy, tsoro halak ne fa”.. Galadima dai baice komaiba ya koma ya zauna yana murmushi. ★)))*(((★)))*(((★)))*(((★)))*(((★ Ganin har anyi sallar Magriba babu baba k'arami balle Dady ya saka Innaro d'aukar gyale ta fito, lokacin gwaggo Safiyya tana salla, shiyyasa batasan innaro ta fitaba, habiba da Naja'atu dake tsakar gida suna tattare kaya saboda hadari na farkon damina dayake nuna alamar zai zubda ruwa. suka kalli juna, Naja'atu tace “yaya habiba tsohuwarnan fa bata da dama wlhy”. Dariya habiba tayi, “ai kad'anma kika gani Naja'atu, yanzu dai zataje ta tadama baiwar ALLAH hankali”. “to ALLAH ya k'yauta”. ‘cewar Naja'atu tana rik'e ha6a’. Lokacin da Innaro ta shigo gidan d'akin Innarsu Munaya ta nufa kai tsaye, sai dai ta iskeshi rufe, kwala kiran sunanta ta shigayi cikin masifa, “Ai'sha!! Ai'sha!! Nasan kina jina, wlhy ki fito kafin yau d'innan igiyar aurenki ta tsinke”. Mamansu yaa Hameed da gwaggon Haleematu ne suka fito, mamansu yaa hameed tace “aiko tafita fa inna, dan gab da magribar nan naga Fadeel ya shigo sun fita, bansan mike faruwa ba dai”. “yaza'ayi kusan mike faruwa tunda anyi k'ulle-k'ullen munafunci, lallai jafaru, wai yau da kaine za'a muzantani hannun mak'iyana, to nikuma naga ta yanda Ai'sha zataje wata k'asa jiyyar Auwalu da raina”........ haka taita zuba banbamin masifa matan gida na saurarenta, daga daddy har baba k'arami suna gidan amma sukak'i fitowa. Jarabar Innaro ta saka kowa na gidan fahimtar mi ake ciki, nanfa hassada da bak'in ciki suka kume zukatansu, dukda kuwa sunsan tafiyar bata dad'i baceba, maman fauziyyace kawai hakan yamata dad'i, koba komai inna ta huta da cin zarafin Innaro koyayane. Sai da Gwaggo Safiyya ta shigo tama Innaro magana sannan ta tafi gida, su matan gidanma sai yanzu suka San da zuwa gwaggo Safiyya d'in. Amma sunso ace innarsu munaya na gida Innaro tayi wannan rashin mutuncin. Hummm😕. **************************** Bayan fitowar su Galadima daga birnin gayu, sun wuce gidane, Nuren kuma yakoma hotel d'in daya sauka. Galadima kawai ne ya shiga sashensu, amma Sauban 6angaren mai martaba ya nufa neman yarima Mahfuz. Munaya na zaune a falon farko tareda sabbin kuyanginta guda uku, (dan bata amince su shiga falonta ba, saita gama tantance su sannan) ba wani hira sukeyiba, d'ayace a cikinsu ke sak'a shine abin ya birge Munaya take kallo, tana kwance cikin doguwar kujera ne, yayinda su kuma su ke zaune a k'asan lallausan carpet d'in falon. Dogarai biyune suka fara shigowa hannunsu d'auke da ledoji, sai kuma mai gayya mai aiki Galadima. Da sauri bayin suka mik'e tsaye, saida ya ida shigowa sannan suka d'urk'ushe a k'asa suna kwasar gaisuwa. A la66ansa ya amsa yana d'aga musu hannu, yayinda idanunsa ke kan munaya da itama ke satar kallonsa Duk d'insu kowa janyewa yayi, yayinda bayin da dogaran suka fice bayan sunkai ledojin falon Galadima. Baice da ita uffanba yafara takawa zai shige, tamkar mai tsoron fad'a tace, “sannu da zuwa”. Ysayawa yayi cak, sannan ya juyo da kansa tamkar mai ciwon wuya ya kalleta, bata yarda sun kuma had'a idoba takuma fad'in “nagode sosai”. “for what?”. ‘ya fad'a cikin isa’. Shiru munaya tayi, ta kasa cewa komai. Shima bai sake cewa komai ba ya taka ya shige abinsa. Harara munaya ta raka bayansa da shi, sai kuma ta sauke numfashi tana tashi itama, bedroom d'inta ta koma, a saman sofa ta zauna tana dafe kai, sosai take buk'atar zuwa sake duba mahaifinta, amma ta kula Galadima bashida niyyar cemata taje, kai itako wannan wane irin abune haka? shi dama gidan Sarautar haka yake bakada 'yancin kanka?, komai saida k'a'ida. tun d'azu kuma take kiran number inna bata d'agaba, tadai kira baba k'arami da daddy sun gaisa ta tambayi jikin Abba, shine ma har suke kuma sanar mata k'ok'arin da galadiman keyi. tabbas hakan da yayi yasata jin farin ciki, koba komai tasan shi adaline, ko anan gaba ragamar shugabanci ta riskesa zaiyima na k'asa da shi adalci. Galadima daya shiga tun a falo yafara k'ok'arin cire navy blue d'in jacket d'insa, ya wullata saman kujera, sassauta belt d'in yayi shima amma bai cireba, ya zauna cikin tsantsar nuna gajiya yana furzo iskar bakinsa, remote ya d'auka ya kunna tv, tamkar ya saita lokaci saiga hoton d'iyar minister mai amsa sunan Farhat ana nunawa, an saka 2.5 millions ga dukkan wanda ya kawota koya bada bayanan sirri akan wanda yasan wani Abu akan 6atanta. Wani mugun tsaki Galadima yaja a zuciyarsa yana fad'in wawaye, saiku k'ara yakai 100millions ba 2 ba, idan ubanta ya shirya kawo kansa gareni nima a shirye nake nabashi shashashar 'yarsa mai zubin ta6arya, ya kashe TV d'in kawai ya mik'e ya shige ciki. Ko ina fes da shi, yasan baida Matsala da Sauban a 6angaren tsafta dama. kayan jikinsa ya ida cirewa ya shiga wanka. Bayan ya fito samu yay yad'an kwanta, dan ya samu Hutu kona 2hours ne, dan yanzu akayi sallar zuhur. aiko kwanciyarsa babu dad'ewa barci yay gaba dashi. Munaya ta jawo wayarta da nufin kuma kiran inna, amma sai taga Ashe credit d'inta yama k'are, kanta ta dafe dan haushi, zuwa can tamik'e domin bin shawarar zuciyarta. turare ta kuma fesama jikinta ta d'auki gyale ta yafa. Ta d'an dad'e a k'ofar d'akin tana tunanin idan kuma ta shiga hasashenta bai zama gaskiyaba ya kenan?, wata zuciya tace kije abinki k'ilama wanka yake. Da sand'a na ida shiga tamkar wata 6arauniya, sai kuma na tuna ai yanada CCTV camera, nutsuwa nayi na daidaita kaina, na koma normal saboda tsaro. Ganin babu abinda naje nema d'in a falo saina zarce bedroom ina wani ciccijewa. Mamaki ya kamani ganinsa kwance a kan gado yana shak'ar barci hankali kwance, hakan yamin dad'i kam. Saida nabi ko'ina na bedroom d'in da kallo, ganin babu alamar akwai camera a nan saina ida shiga, wayoyinsa biyu na ajiye gefen filon dayake kwance, rabin hannun damarsa ma nakan d'aya ya d'ora cikin barci halan?. Dole saina hau saman gadon, dan haka na tsaya tunanin yanda zanyi, banida wata mafita dan haka nahau a hankali, kai kace wata hawainiya ce. Cikin rintse ido da cije la66a nakai hannu zan d'auki wayar d'aya. Caraf aka rik'emin hannu, babu Shiri na bud'e idona zuciyata nawani tsitstsinkewa. Fisgoni yayi na fad'o jikinsa, zafin danaji ya sakani sakin k'aramar k'ara. Ya matseni a jikinsa batare da ya kula miya aikata ba. nikam jikina sai rawa yakeyi, tsorona karya d'auka ko cutar da shi zanyi ma........ maganarsa cikin yanayin barci ta Sani kallonsa. Kad'an ya bud'e idonsa dake jajir, alamar da gaske barci yakeyi, muryarsa a sark'e irinta barci yace, “sata kika koma?”. Baki na tunzuro ina marmar da idanu da suka cika da kwalla, nace “ALLAH ya kiyaye, arafa zanyi”. Kuma matseni yayi har saida na rik'e hannunsa,, yace “wannan ba aro bane sata ce yalla6iya, dan haka dolene ki kar6i punishment”. Jin ya ambaci punishment saina kuma rikicewa, nahau k'yarma ina rantse-rantae da matso kwallan idona. Bai wani saurareni ba ya hau sumbatar wuyana, tureshi nafarayi amma saina gaza, dan haka na koma mintsini, shima a banza man kare😩. Dukna d'auka wasa yakeyi kawai farfaganda Ce danna tsorata, amma saina tsinci ya fara sakin layi, iya yina da rok'o, yakushi, mintsini, ban samu ku6uta ba, saima salonsa yafara tasiri a kaina, nima nai luf harda k'ok'arin maida murtani. saida naji zai kama wata tashar nai azamar tsaidashi ta hanyar fad'in “please yalla6ai camera”. Maganinki ai baby😝, su Galadima akwai bak'in wayo dai🤥😂, idan ta gaskiya za'abi ni banga abin punishment anan ba🤣, dama yadawo 'Yar matsalarsa dai tsautsayi ya kawo mai karanbani dason banza ta fad'a tarko😜🥳😆. **********★******** Koda inna ta dawo saita had'ama su Aryaan kayansu, da nufin su koma wajen mamansu yaa hameed harta dawo. Amma suka tibire akan bazasu jeba, su Uncle yace zaizo ya kaisu wajen Auntynsu. Tun inna na lallashinsu harta kai ga mammakesu suka fara kuka, daga nan sukai barcin dole. Bata fasa had'a kayanba, tagama tsaf ta d'auki akwatin zuwa d'akin mamansu yaa hameed. Su Bintu kawai ta iske a falo suna kallo, Aminu ne yace “innar 'yan 2 ina zaki da daddare?”. Murmushi inna tamasa tana fad'in “kayansu Aryaan ne Aminu........” Bata gama rufe bakiba mamansu yaa hameed ta fito. ganin innarsu munubiya da kaya saita had'e fuska. Inna bata damuba tace “ga kayansu Aiyaan, saisu dawo nan da zama kafin na dawo”. “to”. Kawai mamansu yaa hameed tace tana kauda kai gefe. Ran inna ya sosu, amma sai batace komai ba ta ajiye ta fice jiki a sanyaye. Da murnar Haneeff ya tashi zai d'au jakar yakai d'akinsu, amma sai Maman ta watsa masa harara. babu shiri ya koma ya zauna. Jakkar dai sai anan ta kwana, bata d'auka ba, bata bar 'ya'yanta sun d'auka ba saboda bak'incikin inna zataje jiyyar Abba ba itaba. ALLAH ya k'yauta😡. **************************** Dakatawa yay daga abinda yakeyi, ya bud'e idanu a hankali akan fuskata, murya k'asa-k'asa ya furta “camera?”. Kaina na d'aga masa batareda na bud'e idoba. Bai kuma cewa komai ba ya koma ya kwanta yana furzar da huci mai zafi daga bakinsa, sai kuma ya cije lips yana gyara kwanciya da sake rungumeni kawai. Idona na bud'e a tsorace, azatona zai cigaba ne, sainaga ba haka bane. A cikin kunnene ya furta “barci please”. Kallonsa nayi ta gefen ido sai naga idonsa a rufe, nima banida za6in daya wuce na rufe nawan, dan haka na lumshe kawai. Ni sai barcin ya d'aukeni, amma shi ya k'auracema idonsa, mamakin furicina ya dami zuciyarsa, dama yadad'e yana zargin akwai camera a d'akin nan nasa, sai dai bawai ya tabbatar bane, kuma bai ta6a yunk'urin dubawa ba. da wad'annan tunanin ya cinye lokacin barcinsa har aka kwala kiran sallar la'asar. Bud'e idanunsa yayi akan fuskata, yad'an tsuramin ido nawasu time's, sai yaga barcin yamin k'yau, kauda idonsa yayi cikeda basarwa, saikuma ya janyeni daga jikinsa yana yunk'urin tashi, hakanne ya sakani farkawar nima, na tashi da hanzarina ina gyara rigata, sai kuma na sauka na fice batareda nako waiwayoshi ba. Bina yay da kallo harna fice sannan ya janye yana ta6e baki. Ban kuma jin labarin Galadima ba har dare yayi, nafito wanka ina shirin barci ya shigo, yau dai babu laptop d'in kaddara, dagashi sai phone guda d'aya ma, yana sanye da kayan barci kalar gwaiduwar kwai masu duhu. Zama yay a kujerar dake cikin d'akin, yayinda ni kuma na k'arasa saka hijjab d'in dana jawo, babu walwala ko alamar wasa kwata-kwata a face nashi, dan haka nima saina kama kaina. cikin k'asaitarsa yace “muyi magana mana”. Kallonsa na d'anyi, saikuma na amsa da “ina jinka”. d'ago ido yay muka kalli juna, da ido yay min nuni da bakin gadon. Ban musaba nazo na zauna, amma sai nayi k'asa da kaina ina wasa da zoben hannuna. Maida kallonsa yayi ga zoben danake jujjuyawa, kusan mintuna 4 harna d'auka ya ma fasa maganar, na d'ago na kalleshi. Ya kauda kai gefe yana fad'in, “waya fad'a miki da CCTV camera a d'akina?”. Nima ban kalleshi ba na bashi amsa a tak'aice, “bakai ka saka kayarka ba danni?”. Da mamaki ya kalleni, sai kuma ya kausasa muryarsa, “Munaayaa seriously nake miki magana!”. nad'an razana, amma saina dake, nace “kana nufin bakasan da itaba?”. “idan nasan da ita mizai sani aikata wani Abu na sirrina a d'akin”. da mamaki na kalleshi domin tabbatarwa, tsantsar gaskiya na hanga a idonsa, dan haka na danna yatsun hannuna da k'arfi suka bada sautin “k'asss!, k'asan zuciyata na tunanin minene sirrin nasa?”. Idonsa a kaina ko k'yaftawa bayayi, nima na d'ago mukaima juna kallon ido cikin ido, dukda tsorata danai da hango masifa cikinsu ban janyeba, nafara fad'in “tabbas naga camera a falonka, tana nan saitin hotonku kaidasu momma, inda flower d'in nan take, hakanne yasani zargin kai ka saka kayarka saboda tsaro”. “hummm”. kawai yafad'a yana janye idanunsa, sai kuma ya taso ya dawo inda nake zaune, ganinai kawai ya rungumoni jikinsa, na waro idanu dan mamaki, shikuma ya lumshe nasa tareda sumbatar goshina a hankali, shigar sumbarce tasakani lumshe nawa idanun nima tareda k'ank'ameshi. Cikin kunnena ya furta “i'm proud of you my friend”. Da sauri na waro idanu ina kallonsa, saiya d'agamin gira d'aya yana wani miskilin murmushi, sannan ya tadani zaune shima ya tashi ya fita. Baki da idanu da hanci duk na saki ina binsa da kallo, a k'asan raina ina tambayar mike damun guy d'innan ne wai?. Banida mai bani amsa, dan haka na mik'e na cire hijjab d'in nai kwanciyata. d'akinsa ya koma ya d'akko wani Abu kamar k'aramar ball🎱 ya ajiye saman table d'in gaban gadon, sannan ya manna wani dogon Abu a jikin 'Yar ball d'in, ya d'akko laptop d'insa ya kunna. shiru na kusan mintuna uku ya k'urama abinnan ido, zuwa can yafara wata k'aramar k'ara d'i! d'i! d'i!, sai kuma k'aramar danja ajikin abinda ya manna d'in shima tana kawo haske jaa da d'aukewa. Murmushin takaici kawai yayi, a zuciyarsa yanama ALLAH godiya dabai ta6a kusantar Munaya a d'akin nanba. dan tabbas ga CCTV camera ya gani a d'akin, an sakatane can ta saman wardrobe, yanda ko alama hankalinsa bazai kaiba, baiyi yunk'urin cirewa ba, ya d'auki kayan aikinsa ya koma parlour, dan yaga itakuma tanan a ina take?. yanama shigowa tun'a k'ofar tsakanin bedroom da falon ya gani, baima k'arasaba ya koma ciki, kashe laptop d'in yayi ya d'auke k'aramar ball d'in ya 6oye. Duk wannan hidimar da Galadima keyi Sauban na kwance bisa gadonsa yayi d'ai-d'ai yana kwasar barci. Gyara masa bargo yayi saboda tasowar hadarin farkon damina da iska tafara kad'awa sanyi ya busa. daga nan ya kashe masa fitila ya fita zuwa d'akin Munaya. Ita harma tayi barci, tana k'ank'ame da fillo saboda sanyin hadarin dake busawa, gadon ya hau tareda warware bargon ya lullu6a musu. dai-dai iska ta taso mai azabar k'arfi, a rikice Munaya ta juyo ta k'ank'amesa saboda tsorata. Rik'eta yay sosai yana fad'in “uchh! Karki karyani”. Babu shiri munaya ta bud'e idonta, tana k'ank'ame da shi tace, “wai miyasa bazaka ke kwana naka d'akinba ne?”. “k miyasa time d'in da kikaje India kika gajemin d'akina?”. Shiru tamasa bata amsaba, amma yanajin alamar murgud'a bakinta akan k'irjinsa. “punishment ya tabbata agareki yalla6iya”. Da sauri nace “wlhy a'a, inba hakaba zaka koma saman sofa ne, ai kaima haka kamin a d'akinka”. “uyim Madan tsiwa, to ai nima dankar ki murk'ushemin abin cikin kwan cikin barci yasani kwantawa anan?”. Zan bashi amsa aka kwad'a wata tsawa data sakamu ruk'unk'ume juna babu shiri, sai kuma ruwa ya 6alle. Da wannan damar Galadima yay amfani wajen canja salon kwanciyar tamu, tun ina nuna banaso har salonsa ya sakani sakin layi, (😆anya munaya wannan cikin naki bashine tarkon da Galadima ya d'ana miki ba?😜). Da asuba tashi nayi inata zum6ure-zum6ure, baice dani uffanba yashiga toilet ya tsarkake jikinsa. Bayan yafito nima na shiga. Baki ya ta6e yana wani d'age gira d'aya tamkar ina kallonsa ya fice. Saida nasha kukana sannan nayi wankan tsarki, narasa mike sakani biyema Galadima? insha ALLAH zan d'auki mataki (🤣idan babu abin cikin kwan ba😂, nasan inhar yana nan babansa zaita samun bonus😜). Bayan na idar da sallar ban koma barciba, saina gyara d'akin nayi wanka, shirin fitarma na sake yi yau, dan baba k'arami yacemin k'arfe goma na safe zuwa 11 zasu tafi. Kammalatawa kenan ya shigo, ko kad'an banji alamar shigowarsa ba, saida na gama fesa turare ina k'ok'arin ajiyewa na hango kamar mutum tsaye a bayana. Da sauri nayi azamar juyowa, dayake yana gab dani kad'an ya rage na fad'a masa a jiki, na dai samu nad'anyi baya na jingina da mirror ina tura baki. Ko motsi baiyiba shikam, bai kuma janye idonsa daga kallona da yakeba. Haushi ya kamani, nima nabi jikin nawa da kallo kozanga abin da yake kallon, ganin babu wani Abu daya faru na d'ago na kuma kallonsa, “wai yalla6ai mi kake kallone haka?”. d'an yatsansa d'aya yasaka yad'an shafi girarsa yana gyara tsayuwa, “abin cikin kwan mana”. ‘ya fad'a cikin basarwa’. “ta gefensa na ra6a zan wuce ina fad'in “ai lokaci kad'an ya rage maka ka bar ganin nasa”. Da sauri ya rik'o hannuna, na juyo muka kalli juna, mayun idanunsa ya saka cikin nawa, “kina zaton idan nabar ganinsa kema za'a cigaba da ganinki?”. Guntun murmushi nayi ina janye idona daga cikin nasa, nace “kana zaton kasheni zakayi nima?”. “cire maganar ma zato”. Kallonsa na kuma yi, cikin yanayin da shi kansa bai ta6a zaton ina dashiba nace “saika fara shiri”. Shima a dake yace “dama a shirye nake kullum”. Na murmusa ina k'ok'arin cire hannuna daga cikin nasa, amma ya hanani damar hakan, kallonsa na kuma yi nace “ko har lokacin yayi ne?”. Fisgoni yayi na koma da baya, ya mannani jikin mirror d'in tare da maida hannuna baya ya rik'e, ya matseni da jikinsa, fuskarsa gab da tawa tamkar zai had'a bakinmu, yayinda idonsa ke cikin nawa, wani miskilin murmushin gefen baki yayi, yasaka yatsansa yana zagaya janbakin dake kan la66ana a hankali, cikin muryarnan tasa mai kama da an masa dole ya fara magana cikin karsashi “ko Ubangiji yakanyi hukuncine ga bawan daya bijirema umarninsa, koda ace zubarda wannan cikin kikayi dolene saikin kuma d'aukar wani, zubar da shi na dai-dai da haihuwar yara goma anan gidan kafin na aikaki inda shima ya tafi” ya matsa la66ana da k'arfi, wani zafi ya ratsani saiga hawaye a kumatuna, murmushi yayi, yasaki la66an ya dangwali hawayen a d'an yatsansa, nunamin yay yana fad'in “lallai momcyn abin cikin kwan kin cancanta 100%, amma bayan abin cikin kwanfa akwai k'annensa, please bar kuka my dear friend”. ‘ya k'are maganar da sumbatar la66ana sannan ya sakeni yaja baya. Koda ya sakeni sainayi murmushi kawai, sannan na juya ina fuskantar mirror, foda na d'auka na gyara fuskata, na sake saka jambaki kad'an kamar yanda na saka d'azun. Tsayawa yay cikeda mamakin abin da nayi na ko inkula yana kallona, mi wannan yarinyar take shiryawa ne haka?..... Kafin ya samu amsa Na juyo gareshi, fuskata d'auke da murmushi na ra6a zan wuce sa, bina kawai yay da kallo, naje gaban wardrobe na bud'e, alk'yabba na d'akko na sanya, sannan na d'auki handbag ina kallonsa har yanzu fuskata d'auke da murmushi. Gira ya d'agamin shima yana wani k'asaitaccen murmushi, ya juya ya fita batareda yakuma magana ba. Yana fita na sauke ajiyar zuciya ina dafe k'irji, wlhy ni kad'ai nasan dukan da zuciyata takeyi, kad'an yarage ya ranfo a tsorace nake, kalamansa ne suka shiga dawomin cikin zuciyata, mi wannan yake nufine wai..........? “Shin bazaki bane?”. Muryarsa ta daki dodon kunnena, da sauri na gyara yanayina na d'ago muka had'a ido, Ashe yana bakin k'ofar bai tafiba. Bance komai ba na biyo bayansa. A falon farko na iske kuyangina suna gaidashi, hannu kawai ya d'aga musu ya fice abinsa. Tsayawa nayi muka gaisa, d'aya a cikinsu ta yunk'urin k'ar6ar handbag d'ina. Na iske harya shiga mota, nima aka bud'emin na shiga, handbag d'ina ta mik'omin tana fad'in “ranki ya dad'e ana buk'atar rakkiyarmu ne?”. Murmushi namata, na juya na kalli Galadima danjin mizaice, kansa ya girgiza alamar a'a. Juyawa nima nayi na girgiza mata kai, tamana addu'a tana rufe k'ofar. Tunda muka tafi babu wanda yace uffan, yanata latsa wayarsa. Airport muka nufa kai tsaye. Bayan motocin sun tsaya sarkin mota na yunk'urin fita yace “2 minutes ”. Sarikin mota yace “to ranka ya dad'e”. Ni ban fahimci mi suke nufiba, naga dai sarkin mota ya fita mukuma ba'a bud'e mana ba, sai kawai nakai hannu zan bud'e. Hannuna ya rik'o, na juyo ina kallonsa, har Yanzu idonsa nakan waya,, ajiye wayar yayi ya juyo yana fuskantata, ina yunk'urin tambayar lafiya naji la66ana cikin bakinsa. Ya salam, na fad'a a zuciyata, saida ya shanye janbakin la66ana tas sannan ya sakeni. yanda kukasan gunki haka na koma masa, ya buga yatsunsa biyu saitin fuskata suna bada k'arar d'as d'as yace “gargad'i, first and last dazanganshi abakinki yayin fita”. Harya fita ban iya motsawa ba, saida aka bud'e murfin 6angaren danake sannan na iya sauke numfashi, na kasa fahimtar damuwar guy d'innan kwata-kwata. fita nayi nima, yana tsaye yana jiran fitowata. a tare muka jera muna tafiya, yayinda dogaransa ke take mana baya. ya wani miskile fuska tamkar bashine yagama ta6argaza ba a mota yanzun. Mutane sai kallonmu suke, masu gulma nayi masu nunamu nayi, ni dai duk sainaji wani iri, shima tsaki yayi danya tsani kallo. A mamaki na duk sai naga 'yan gidanmu ma a wajen, gaggaisawa muka shigayi, muka rik'e hannun juna nida munubiya muka k'arasa inda innarmu take, gaisheta nayi, nace “su Aiyaan fa?”. “suna gida zasu zauna da mamanku mana”. “kai innarmu, ya zaki barsu wajen muguwarnan, bama gara Maman fauziyya ba komu suzo wajenmu”. Murmushi kawai innarmu tayi, tace, “ashe bazaki canjaba Munaya?”. 6ata fuska nayi, ina fad'in “kai inna, duk canjawarnan danayi”. Murmushi sukayi itada Munubiya. akuma dai-dai time d'in Ambulance ta shigo airport d'in, sai mota biyu a bayanta sai motar police guda d'aya. Gaba d'ayanmu hankalinmu saiya koma can, Galadima ya k'arasa wajen Ambulance d'in, yayinda sauran motocin biyu Sauban da Nuren baba k'arami Dady ya Shafi'u da yaa Naseer yaa hameed suka fito. Zuwansu baifi da mintuna 15 ba aka fara kiran sunan wad'anda zasu tashi a jirgin. Sai kuma ma'aikatan wajen mutum uku suka iso wajen Ambulance d'in aka fara k'ok'arin fidda Abba. Hankalin jama'a da yawa ya tashi a airport d'in nan saboda tausayin Abba, mukam kuka ma wasunmu sukeyi ai, muna kallo aka gungura gadon da aka d'oroshi har zuwa ga jirgin. Suma su innarmu suka shiga itada baba k'arami da Sauban. Rungume juna mukayi nida munubiya muma muna kuka. Galadima bai fito cikin jirginba saida yaga komai ya dai-daita. yana fitowa babu dad'ewa jirgin ya d'aga zuwa sararin samaniya, yayinda mukuma muke binsu da addu'oin fatan alkairi da samun sauk'i.................✍🏼 🤥kutt harda na gobe nayi🙄⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_* *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣2⃣ ...............Maman Fauziyya tamatso ta kama hannunmu ni da Munubiya tana lallashinmu, da fad'a mana mu bisa da addu'a, insha ALLAHU da k'afarsa zai dawo. Ganin mun fara shirin tafiya na taka inda Galadima yake tsaye da Nuren suna magana, tun d'anzun ina lura dashi ya kafeni da idanu, yanzunma suna maganar amma idonsa na kaina na k'araso garesu. Nuren daketa fara'a yace, “gimbiyarmu barka da hantsi”. Murmushi nayi sannan na gaisheshi, ya amsa yana tambayata yaya jikina?. Nace “Alhmdllh na warke ai”. “to ALLAH ya k'ara afuwa gimbiya”. ‘yafad'a yana matsawa gefe domin bamu waje. Galadima dake kallona hannunsa duk biyu cikin wandon sky blue d'in shaddarsa da tsawon rigar iyakarsa rabin cinyarsa, yace, “Lafiya?”. Dakewa nima nayi, cike da jan ajina nace “k'alau. Dan ALLAH zanbi Munubiya please yalla6ai”. Janye idanunsa yayi daga kaina yana fad'in “awane farashi?”. “kamarya farashi? ciniki mukeyi?”. Hannunsa d'aya ya fiddo daga aljihu ya shafa sajensa zuwa gemu, cikin kafeni da idanu yace “kusan haka, kinsan rayuwar bani gishiri in baka manda akeyi yanzun”. Cikin son tura masa haushi nace “Ai ni bana gane Hausa cikin hausa”. “really? lallai kin fad'o kuwa, kuma saiki ce ke bahaushiyace?”. Baki na tunzura masa saboda haushin rainin wayon da yake min, gasu Munubiya kuma shirin tafiya sukeyi. “Kinsan wannan bakin kika bari na kamashi a airport d'innan....., hummm”. Idanuna na waro, “mi kake tunanin zakayi kenan?”. “kuma turowa saina nuna miki”. ‘yafad'a yana matsowa’.. Baya na matsa da sauri zuciyata na harbawa, anya kan Galadima d'aya kuwa?. Kwafa yayi yana kallon agogon hannunsa yana k'ok'arin zaro waya daga aljihun gaban rigar datake ring. Nikuma na hararesa a zuciyata ina fad'in mara kunya ai nasan zaka iya. A fili kuma nace “please yalla6ai nidai badan halina ba”. Bai bani amsaba, sai sallamar danaji yayi wayarsa akan kunne. Jinai kawai yace, “Harun kana inane?”. Bansan wace amsa ya bashiba, naji yana fad'in “ok idan ka tashi saimu had'u”. daga haka ya yanke wayar sannan ya kalleni. “uhm mikike cewa?” Haushi tamkar zai karni nace “please mana autan Momma”. Murmushi yayi yana cije lips, “wlhy yarinyarnan kin gama rainani, ninema Autan?”. “lah nama manta ashe kaifa na tsakkiyar momma ne, karma Yaa Sauban ya jini”. “kinsan ALLAH na damk'eki a airport d'innan saikin fad'amin dawa kike”. Dariya nayi ina d'aga masa yatsu biyu, “karka damu yalla6ai zanyo maka tsarabar sweet and biscuit yeah”. Da sauri yay yunk'urin damk'o hannuna ganin zan gudu. yana rik'owa mukaji ance “hallo”. A bayanmu. Batareda ya saki hannuna ba duk muka waiga ni da shi. Matashiyar budurwa fara k'al, kuma k'yak'yk'yawa masha ALLAH. Dan danan ya tsuke fuska, tamkar ba shine yagama murmushiba yanzun. Nima bansan murmushi ya gushema tawa fuskarba, baiyi magana ba, sai nice nace “lafiya kuwa?”. yanda nayi maganar cikin rainin hankali yasaka yarinyar rik'e ha6a tana ta6e baki tana fad'in “ke kuma fa?”. Kamar zanyi magana saikuma Na shareta kawai, galadima Na kalla fuskata a cunkushe alamar fushi, d'ayan hannunsa ya d'agamin yana ta6e fuska alamar shifa babu ruwansa. Na tura baki tareda juyawa zan bar wajen. Hannuna dake cikin nasa ya kuma damk'ewa da k'yau, hakan yasani dawowa baya tamkar zan fad'a jikinsa, amma nayi jarumtar tirjewa kodan jama'ar gidanmu. Dama ajikin wasu motoci muke, sai kawai ya fisgi hannuna muka shige tsakkiyarsu ya mannani jikin mota shikuma yamin rumfa. ban ankaraba naji bawan ALLAHnnan ya ha.......🤥. Jikina kawai rawa yakamayi saboda tsoro, wlhy ban ta6a tunanin da gaske yake zai iya hukunta bakin nawa a airport d'inba. Ita kanta budurwarnan idanu ta zaro waje cikin wangale baki. Nuren dashi kad'ai yake saitin dazai iya ganinmu saikuma wasu tsirarun mutane dake nesa damu, wad'anda ba lallaine ma su fahimci abinda akeba, kaucewa kawai yay daga wajen yana tuntsura dariya. 'Yan gidanmu sunga lokacin da Galadima yaja hannuna muka shige tsakkiyar motocin, amma basa hangomu. tsabar gulma irinta mamansu Yaa Hameed da Momy da Maman Safara'u sai suna shiga k'ok'arin son ganin mi mukeyi a wajen?😱 su duk tunaninsu wata maganar banza nama budurwarnan yake shukamin rashin mutunci Dan duk agaban idonsu tazo wajen har rik'omin hannu da yayi, dukda basa jin mi Muke fad'a Dan muna nesa dasune. Yaa Sabi'u dabasu lura da abinda ke faruwa ba suka Shiga musu maganar INA zasuje? suzo su ajiyesu gida sufa wajen aiki zasuje. Ina basu saurareshiba saida sukazo saitin dazasu iya ganinmu. A tare suka zaro idanu, Baki da hanci, duk sun shiga mamakin ganin Galadima Na kissing d'ina, ai babu shirin suka koma baya zukatansu Na tukuk'i da jifanmu da kalmar 'yan iska fitsararru. (🤣Yo wayace kuje gani? kazantar dabaka ganiba sunanta tsafta😏😜). Yana Sakina kunya tasakani fad'awa k'irjinsa Na 6oye fuskata, hannayensa yasaka ya zagaye bayana yana dallama yarinyarnan wata muguwar harara data saka hanjin cikinta kad'awa, babu shirin tabar wajen tana mak'yark'yata da tunanin Galadima ko dai kurmane da gaske. Driver d'inta dake kallon komai tun d'azun ya tuntsure da dariya yana fad'in ALLAH ya k'ara, bana fad'a miki Shiba Na wasan yara bane ba, banda jaraba kinbi kin nanik'ema bawan ALLAH daga had'uwa a jirgi, kinbi kin addabi rayuwata saina nemo miki number sa, aini nama godema ALLAH da kuma sake had'uwa ya kuma nuna miki ainahin halinsa, saida Na fad'a miki baima dad'e dayin aureba, ke gadararriya kikace aurensa bai damekiba........ Yanda ta daka masa tsawa yasakashi firgita ya russuna yana Neman afuwarta. Cikeda masifa tace “tada mota mukoma gida”. “Amma ma'am kin manta jirginku yakusa tashi?”. A tsorace yayi maganar. Harara ta Dalla masa tace “Ubanka ne ya viyamin kud'in jirgin”. Wasu yawu masu rad'ad'i driver ya had'iye yana girgiza mata kai, ya bud'e motar ta Shiga sannan ya rufe shima ya zagaya mazauninsa suka koma Inda suka fito😜. Nasan dai kun fahimci yarinyarnan Ce da suka zauna waje d'aya a jirgi itada Galadima randa zaizo😆🥳. Ganin tabar wajen Galadima yay murmushi sannan yafara k'ok'arin d'agoni daga k'irjinsa, ban yarda mun had'a idoba na bar wajen. “Saikin dawo” ya fad'a a hankali. Kasa daurewa nayi saida Na waigo Dan tabbatar da shine yay maganar kokuwa dai wanine?. Ido muka had'a ya janye nasa cikeda basarwa yana la6e baki. Nima harara Na watsa masa ina barin wajen. Tunda Na taho Maman safara'u da mamansu Yaa hameed da Momy suka zubamin ido. Nikuma fahimtar kallon k'urillar da sukemin saina canja salon tafiya da kuma had'e fuska na nufi zuwa wajen gungun yaran gidanmu masu aure dasuke hira. Suma duk kallona sukayi, namusu murmushi ina fad'in “lallai munada cin ragunan suna kwannan nan ashe”. Dariya duk sukayi, Fiddausi tace “yariman namu shikuma da kwad'ayin naman suna yazo?”. Harara Na zuba mata ina kai mata bugu ta waske itama tana dariya, yayinda su Munubiya ke tayata. Mun gaggaisa tareda tambayar lafiyar juna, muka d'an ta6a hira kad'an da alk'awarin duk zanje mu gaisa, suma sukace zasuzo tunda ba yanzu zan koma ba. daga nan mukai shirin tafiya, Siyama da Zarah anata mana iyayi su masu motar hawa, (dayake kowacce a motarta tazo). Ni dai ni da Munubiya Yaa Marwan ya d'aukemu muka tafi. ____________________________ Tunda nabar wajen Nuren yazo ya tasa Galadima da tsiya, wai dama haka yake ashe?, rashin kunyar tasa har agaban surukai?. Banza Galadima yamasa yay shigewarsa mota yabarsa yana iskancinsa. Anan suka tafi suka barsa dayake da mota yazo shima. Galadima na barin airport gidanmu ya nufa shima. A lokacin 'yan gidanmu suma sun Isa gida, sunata k'ananun magana akan abinda Galadima da munaya sukayi, dan saida suka bama sauran labari, nanfa suka kacame da zancen harda k'arin k'arya akai wai ba kiss kawai sukaiba ('yan gidansu munaya annamimatu🙆🏻😂). Itadai Maman Fauziyya batace k'alaba, saima dariya da zancen ke bata, Dady kuma bai dawo gidanba, daga nan wajen aiki ya wuce, yaran gidan ma kowa gidanta ta koma basu biyo nanba. Innaro da gwaggo Safiyya kam gida suka shige ana saukesu, dan haka basuji komaiba. Galadima bai shiga gidan ba, saiya nemi iso gidan Innaro, Habiba ta fito tamasa jagora. Innaro na falo tana cika da batsewa gwaggo Safiyya na lalla6ata akan ta kwantar da hankalinta. Koda Galadima ya shigo innaro sai antaya masa harara takeyi, yana kula da ita ta gefen ido, ya murmusa yana zama saman kujera, cikeda tsokana yace “Sweet Granny Yaya dai?”. Harara innaro ta zuba masa sosai, tana fad'in mikuma kazo min nan?”. Galadima ya murmusa yana maida hankalinsa ga gwaggo Safiyya, gaisheta yayi ta amsa masa cike da kulawa, sannan ta d'ora da godiya da kwarara masa addu'ar fatan alkairi. Yaji dad'i sosai, ya amsa cikin fara'a, sannan yace, “Granny ina furar tsufa?”. “ai bazaka shata ba ”. Nanma murmushin Galadima yayi yana mamakin wannan rikitacciyar tsohuwa. Yace “tunda bazan shaba Ashe kema kuwa bak'yaje India ba”. Zabura innaro tayi, ta maida hankalinta ga Galadima tana fad'in “da gaske kake ko shak'iyancine?”. Mi su Naja'atu zasuyi inba dariya ba, Galadima ma handkerchief ya saka ya rufe bakinsa kawai. Gwaggo Safiyya kanta saida ta dara. Galadima ya gyara zamansa yana fad'in “karki damu Granny ninmu, insha ALLAH tare dake zamu tafi idan zamu koma”. Dad'i ya kama innaro ta shiga sakama Galadima albarka. Shidai murmushi kawai yakeyi. saida yaga sun nutsu sannan yace yazo tafiya dasu Aiyaan ne, babu musu innaro ta mik'e da kanta zuwa gidan danta kawo masa su. Bayan fitarta gwaggo Safiyya tabama Galadima hak'uri akan darun innaro. “karki damu gwaggo, ai dama kowa yasan idan sunkai irin wannan age d'in saida lalla6awa, ALLAH dai yaja mana ransu”. Amin gwaggo Safiyya tafad'a cikin jin dad'i. Tunda 'yan gidansu Munaya sukaji wai Galadima ne da kansa yazo tafiya dasu Aryaan sai zukatansu suka kuma tunzura, kowa tana ganin hakan salon munafurcine, Maman Fauziyya ta kawoma innaro su, dama suna d'akinta, dan mamansu yaa hameed suna dawowa ta d'auki jakkarsu Aiyaan ta kaimata, wai sai dai su zauna wajenta ita d'akinta babu fili. Maman Fauziyya batace komai ba ta kar6i su Aiyaan tana jinjina bak'in hali irinnan jama'ar gidan. Amma kuma yanzu sai gasu sune dajin haushi. Ita dai innaro ko'a kanta ta jawo hannunsu Zainab ta d'akko jakkar kayansu suka taho. Koda sukazo ma sai Galadima yace abar kayan nasu su kad'ai yake buk'ata. ya ajiyema Gwaggo Safiyya da innaro alkairi ya fito rik'e da hannun su Aiyaan daketa murna. Innaro har wajen mota ta rakosu, bata komaba saida taga tafiyarsu. tana komawa gida tahau had'a kayan tafiya, wai gara ta had'a ta huta, duk randa Galadima yazo sai tafiya kawai. Ita dai gwaggo Safiyya dariya kawai tayi, dan maganar Galadima gaskiyace, lamarin innaro yana buk'atar uziri, ta tsufa sosai, kawai dai ALLAH yabata lafiyane, dan da wuya kaga innaro na kukan wani waje namata ciwo irin na tsufa. (masifarta kam dai kunsan ance abinda kayi a k'uruciya shi kake maimaitawa lokacin tsufa, ALLAH ka azurtamu da k'yak'yk'yawar k'uruciya to🤦🏻‍♀). ★★★★)(★)(★★★★ A k'ofar sabon matsakaicin gidan motocin biyu suka tsaya, cikin wad'anda suke a motar baya d'aya ya fito ya bud'e motar farko, hamshak'iyar macece mai ji da mulki da kud'i ta fito, kallo d'aya zaka mata ka tabbatar tagama samun duniya, cikin tsantsar tink'aho da homa take zuk'ar iska tareda taku d'ai-d'ai irin na manyan mata. Cikin sauri aka bud'e mata k'ofar gidan ta shiga guard d'inta na take mata baya. A tsakkiyar tsakar gidan taja tunga, sai hura hanci takeyi tana harare-harare. d'aya a cikin guards nata yace, “ ma'am nan shine d'akin da yake”. Batace uffanba taci gaba da takawa d'ai-dai har zuwa k'ofar d'akin, hannu ta d'aga musu alamar su dakata. Dukkansu baya sukaja domin cika umarninta. Zaune yake a kujera an d'ad'd'aureshi, kallo d'aya zaka masa ka tabbatar a galabaice yake. Shigowarta baisa ya d'aga kai ba balle ya motsa, yasan dai bazai wuce k'artan dasuka kawosa wajen baneba. sai dai jin k'amshin turaren mace yabashi mamaki, hakanne ya sakashi d'ago idanu domin tabbatar da yaren hancinsa. Bakinsa na rawa yace, “Wacece ke?”. Bata bashi amsaba, saima kujera data ja irin wadda yake kai ta dinning ta zauna, k'afa d'aya ta d'ora akan d'aya tana wani cika da batsewa. “yaro baka isa sanin ni wacece ba, Sai dai cigaba da 6atamin aiki zai sakaka sanina”. Murmushi Muftahu yayi, ya d'ago idanunsa yana mata kallon rainin wayo, “Saninki dama aikin banzane a gareni, aikin ki kuma da kike ik'irarin ina 6atawa duk da ban sanshi ba, kisa a ranki yanzu ne na fara 6atawa, saiki shirya nunamin ke d'in wacece?”. “hahaha, yaro baisan wutaba saiya taka”. “Humm, wuta bata san yaroba saisu k'ulla”. “karan farauta yaushe uban gidan naka yafara koya maka irin izzarsa haka?”. “Kinsan zama da mad'aukin kanwa aishi ke kawo farin kai”. “lallai zan had'a da kanwar da mad'aukin nata duk na koyar dasu darasi. Shi kansa Sameer d'in baikai darajar karen gidana ba balle kai yaronsa”. Murmushi Muftahu yayi, “ Uhmm sai yanzu na fahimta, sai dai zan tunatar dake abinda kika manta, Wanda kikeyi danshi baima San da zamanki ba, kinga ashe ihu kikeyi bayan hari..........”. “hhhhhhhh! Abin dariya, inbai fahimta ba ai zai fahimta lokacinda sak'on sunana da gawarka suka isa a gareshi, yanda ban haifi magajin masarautar gagara badauba, zeenah bata isa haihuwar magajinta ba wlhy”. Idanu Muftahu ya tsura mata, sai yanzu yafara hango kamannin d'aya daga matan tsohon Sarki Abie da suka bar masarauta bayan shekaru biyu da fara jinyarsa, bashida wayau a time d'in, Dan dagasu har Galadima bazasu wuce 7-7 year's ba, saida suntaso sunji labarin bijirewar matan a lokacin da za'a tafi da Abie India, dama shekaru biyun da suka zauna basu ta6a saka hannu a jiyarsa ba, sai Momma keta fama........... Marin da aka zuba masane ya sakashi dawowa daga dogon tunanin daya tafi.... “tunanin mi kakeyi Karen farauta?”. Jajayen idanunsa ya zuba mata, sai kuma ya kwashe da dariya, saida yayi mai isarsa sannan ya dakata tareda tsuke fuska, “ina tunano mummunan fuskarkine, in banda abinki miye na kishi da abinda kika bari da kanki? nasan dai Momma ba itace ta hanaki haihuwa ba ai, inason kisan ni ban isa kare Galadima ba dama, amma kulum cikin kariyar Wanda ya haliccesa yake, a tunaninki 6ata sunansa da kikayine ke nufin bazai mulki masarauta mai d'unbin tarihi da girmaba? kinyi kuskure babba wlhy, Dan kinsaka kanki a ramin damisa. duk ranarda Galadima ya gane kece kika saka amasa 6atanci a jarida wlhy saikinyi nadamar rayuwarki.......... Bayan Hannu tasaka ta bugi bakinsa, gefe yay da kansa yana murmushi, ga jini na zuba a gefen bakin, dayake hannunsa a d'ure suke. Tace, “kafin ni nayi nadamar kai ne da shi zakuyi, Dan yanda kake a tarkona shima yanacan a cikinsa, wawa kawai, kai aboki mai gaskiya ko? zan shayar dakai mamaki, domin saikaga gawar Sameer a gabanka kwance kafin kaima kabishi baya”. Dawo da kallonsa yayi gareta yana murmushi, “miyasa kika tsorata tunban k'arasaba, Galadima maruci ne, kuma kainuwane, gashi dakalin majina, kina hawansa zamewa zakiyi wlhy, ina tausaya miki yayinda tunaninsa ya waiwayo kanki, Dan yanzu aikin manyanki ne a gabansa ba nakiba, d'ana masa tarkonki kuwa tamakar kin tado damisane daga barci, hakan kuma fitinace babba a gareki da shi kansa Karen farautar taki Harun, tirrr da zuciyarki, ni kaina danasan ma kece bazan 6ata lokacina wajen bibiyar ki ta hanyar Harun ba, amma banyi bak'in cikiba, ko babu komai na ribantu da abubuwa masu yawa, domin ta silar hakan na had'a auren sunna, gashi harda ribar ciki, magajin Galadima Sameer kenan....... A fusace ta d'aga kofin glass zata kwala masa. Yace, “relax relax mana giwar mata, ai bangama fad'aba OK?” ba kince zaki kawomin gawar Galadima ba sannan, to miye kuma na fusata haka da wuri?, ni ina kuma tabbatar miki indai Galadima ne zaizo, daga lokacinda yasan ina nan tabbas zai zo, banza karyar farautar wasu, na tabbata k'arya kikeyi ba aikin kanki kikeba kema, sakaki akayi, lallai ke farashinki ya fad'i k'asa, matar sarki mai fad'a aji irin Sarki Saifudden Ce ta k'are ahaka? Abin kaico abin jaje, tirrr”. Dariya ta kwashe da shi tana tafa hannaye, saikuma ta matsa gabda Muftahu tana magana cikin kunnensa “lallai bayan Sameer akwai magajin sa a gagara badau ashe?”. “oh sai yanzu kika fahimta ashe?”. “karen Sameer zaka mutu kaida uban gidan ka, saina saka wannan zuciyar tasa ta buga wannan shine k'udirina”. “hhhhhhh abin dariya, kudirin wasu dai, danke naki bamai muhimmanci baneba, tunda kuka kasa saka zuciyar Sameer bugawa a lokacin da k'uruciya da rashin sanin kansa ke damunsa, miyasa kuke tunanin zata buga a lokacin da yagama tanadar makaman yak'insa, ranar shiga filin daga kawai yake jira, nagaji da tattaunawa dake please”. “kaima kace wani Abu yaro, Dan haka mu zuba, kwana uku kawai zakaga gawar Sameer a gabanka!!!!!”. Bata jira yabata amsaba ta fice daga d'akin, tareda jan k'ofa da k'arfi. Idanunsa kawai ya rintse. Baya tsoron makircinta, amma yana tsoron na Harun, dan Galadima ya rigada ya yarda da Harun 100%, bazai ta6a kawo zai cutar da Shiba. Waige-waige yashiga yi, yasan babu wani abunda Galadima zai iya bibiya tare dashi. Da sauri ya girgiza hannunsa saboda tunowa da agogo, jin agogon tare dashi ya sakashi lumshe ido yana ambatar Alhamllh. Matsala d'ayace baya ganin agogon, saboda hannunsa yana a baya ne. Amma dukda haka zai gwada idan za'a dace. ___________________________ Yau na kasance cikin farin ciki, saboda gani tsakkiyar 'yan uwana, dukda ma zazza6ine mai zafi ke nuk'urk'usata, amma kewarsu ta hanani gajiyawa, mun bud'e babin fira a tsakkiyar falon mama Rabi'a, duk abinda akayi bana nan shine ake labarta min, yayinda Nima nake basu labarin India da nuna musu hotuna. Haka mu kai wannan yini cikin farin ciki da annashuwar kasancewa da junanmu, musamman ma ni da 'Yar uwar tagwaicina da k'addarar aure ta tilasta mana nisantar juna, ji muke tamkar mun shekara ba'a tareba. Kowannenmu k'ok'arin ganin farin cikin d'an uwansa yakeyi. _____________ Tunda Galadima yabaro gida dasu Aryaan saiya wuce wajen wani hutawa dasu, ya yawata dasu sunata farinciki, yayinda shi kuma yake biyema shirmensu dan d'auke musu kewar mahaifiyarsu, yana son yara, shiyyasa ko yaushe Khaleel d'in aunty Mimi zakigansa manne dashi, sa'annin Khaleel dasu Aiyaan kuwa zai iya zuwa d'aya. Cikin lokacin k'ank'ani suka saki jikinsu dashi. Daga nan plaza ya nufa, haka kawai zuciyarsa keta tsikara masa zancen 6atan Muftahu, dukda k'ok'arin wofantar da lamarin da lamarin da ya keyi. Waya ya d'auka ya shige danne-danne, alamu sun nuna masa wayar Muftahu na cikin masarauta, kenan bai d'auki wayarba, yad'an murmusa kawai yana cije lips, yayinda idonsa ke kansu Aiyaan da Saleem yazo d'auka suje wajensa danya huta. Bye suka masa, shima ya d'aga musu hannu yana murmushi. Suna ficewa ya sauke ajiyar zuciya tare da mik'ewa tsaye. zagayen office d'in ya farayi hannunsa goye a baya, a wannan karon bazai ta6a k'yale Muftahu ba, dolene yayi wani Abu akansa, dama yana d'aga masa k'afane domin son ganin gudun ruwansa kawai, yanzu kuma lokacin yayi dazai San mi yake k'ullawa...........✍🏼 *_Duk Wanda yaga ban amsa massage nashiba yamin afuwa, cakwakiyar network tasani clearing charts d'ina batareda na dubaba, tun around 3:47pm nayi posting amma yak'i tahowa._* Dan haka ina gayyata kowa gobe a court, zamu shiga shari'a ni da network ne🙄. Wad'anda suka ga basa ganin posting d'ina gaba d'aya a satinnan duk aikin network ne🙄. *_ALLAH ya gafartama iyayenmhiyayenmu😭🙏🏻_* *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣3⃣ ...............Muna tsaka da hira saiga Aunty salamah tazo, daga ni har Munubiya da Ayusher rungumeta mukayi. Cikin tsokana ta ture Munubiya da Ayusher tana fad'in “ku matsamin, kullum Ku ina ganinku, kewar gambo nakeyi”. Gwalo na shiga yi musu, mama Rabi'a da Feena namana dariya. Bayan mun zauna Aunty Salamah ta shiga yaba canjawar danayi tanamin shak'iyanci, nanfa su Munubiya ma suka samu abinyi, sosai suka tasoni gaba sai mama Rabi'a ke kareni. Can muna tsaka da hira takamo hannuna tana fad'in “zo nabaki wani sirri nan autana”. Mik'ewa mukayi inamasu Ayusher gwalo, yayinda suma suka tubure basu yardaba sai an bada sirrin dasu. da k'yar muka samu muka shige d'aki muka kulle. A bakin gado muka zauna Aunty slamah ta sauke ajiyar zuciya tana kamo hannuna cikin nata, serious nima na zama na maida hankalina gareta. Tace, “Munaya! Aiki yatafi yanda ya kamata, saidaifa labarin ya canja daga yanda kike zato, Muftahu ba munafuki baneba”. A matuk'ar razane naja baya ina ture hannunta daga cikin nawa, “Aunty kinsan mi kike fad'a kuwa? Anya yaranki Muftahu suka kama?”. Hannuna ta kamo tana murmushi, kinga zauna, shiyyasa na saka aka d'auki komai dan kema ki gani da idonki”. Zaman nayi kuwa, ita kuma tayi 'yan latse-latsenta a iPad d'inta ta mik'omin. kar6a nayi cikeda fargaba, da kaina nayi playing d'in video n, tun daga fitowar Aunty salmah daga mota har shiganta cikin gidan zuwa shigarta d'akin, tsayarwa nayi na kalli Aunty ina dariya, “kai Auntynmu kinfa iya Acting wlhy, wanifa saiya d'auka da gaske irin mugayen hamshak'an matan nanne”. Dariya Aunty Salamah tayi, “wlhy koni dai nayi mamakin dakewata, bakiga sai wani hura hanci nakeba, sukuma su Ameer saikace guards d'in irin manyan mutanan nan”. Dariya mukayi, sannan nakuma playing na cigaba da kallo. Shigar Aunty Salamah d'akin da tattaunawarsu da Muftahu. gaba d'aya jikina yayi sanyi, zuciyata sai wani tsitstsinkewa takeyi, idona cike da kwalla nace, “anya gaskiya Muftahu yake fad'a Aunty Salamah?, wlhy da gaske fa shine ya saka mana desire tablets, inhar bada wata manufaba miyasa yay haka?, kumafa ni banta6a ganin wani alamar rashin gaskiya ba ajikin Harun”. Murmushi Aunty Salamah ta yi, ta dafa kafad'ata tana fad'in, “Munaya mugu bashida kama, Ai Muftahu baisan nid'in ba matar sarkin bace ta gaske, mizaisa ya za6i 6oyemin? yanda yanuna akan k'yamar matar sarkin tabbas akwai mai mugun hali a cikin su da gaske, kinga ai kince bakiga fuskar wanda kika kama yana wayarnanba a bayan window d'inki randa kuka iso”. “Eh hakane, ban ganiba, maganganun kawai naji”. “to kin gani, kifa tuna kuma firar da kika ta6aji Galadima nayi a asibiti shida aunty Mimi. wad'annan alamomin sun nuna akwai wata a cikin matan Sarki dakeda hannu a ciki, maganar Harun kuma idanu zamu saka masa tamkar yanda mukaima Muftahu, dan ayanzu idan mun saki Muftahu zakiga sun cigaba da takun sak'ar datafi ta da zafi, dan nariga da nasaka rud'ani a zuciyar Muftahu cewar zamu kashe galadima, tabbas ta wannan hanyar Harun zaizo hannunmu. Maganar Galadima kuma har yanzu karki fara kwantar masa da kai, dan kwantar da kanki zai d'arsa masa rashin aiminci a kanki, ke dai kinsan halin mijinki ai yanzu, kinkuma fi kowa sanin yanda yakamata ki cigaba da tafiya da shi”. Insha ALLAH Aunty zan cigaba da k'ok'ari nakuma gode da gudunmawarki akanmu, sai dai akwai matsala, dan na lura agogon hannun Muftahu kamar akwai wani sirri a cikinsa, dolene a daren yau a fitar da Muftahu daga gidanan, zanma sarkin mota bayanin yanda zai taimakeku a maidashi masarauta kamar yanda yaymana aikin d'akkoshi, shima Galadima zansa ido akansa saboda tsuntsune shi nai azabar wayo”. “Hakan yayi Munaya, ALLAH ya cigaba da bamu nasara, insha ALLAH zamu gano komai, ALLAH dai yabama Abba lafiya, yasa mu fahimci komai cikin sauk'i, akan Galadima kuma kici gaba da k'ok'arin da kikeyi Fiyeda da, dan dolene saimun samu had'in kansa kafin musan komai, ALLAH ya ku6tar damu baki d'aya, dan kina dai ganin yanda suka maida Abba”. Hawayen da suka ziraromin a kumatu na share, cikin Murmushin k'arfin hali nace, “insha ALLAH Aunty Salamah, domin raina da farin cikina fansane akan mahaifina, kuma zuwa yanzu Auren Contract bai damuna, sai dai bazan 6oye mikiba aunty Salamah wannan cikin shine damuwata a yanzu, inaji ina gain zan haifishi na barsa inda yafi k'arfina, bansan wace rayuwa zaiyiba a wannan gidan da kowa zuciyarsa takeda k'arancin imani, Aunty Salamah gidan sarauta tsantsar matsalace kawai, bazaki fahimci hakaba saikin tsinci kanki a ciki, Aunty dan ALLAH ki amince na zuba da cikinnan”. “munaya waishin miyasa bakida hankaline? to idan baki saniba wannan cikin shine zai zamemiki tsanin mallakar cimma nasara, kuma ta hanyarsane kawai zamu samu had'inkan Galadima domin fidda Abba daga wannan matsalan da Ku kanku ahalinsa, kina tsammanin koda Abba mutuwa yay masu farautar rayuwarsa zasu barku Ku6utane? Dolene saisun samu abinda suke nema koda ace dukkan gidanku zai k'are, bak'ya tunanin aurenku yana cikin abinda yakuma hasala zukatansu, a zatonsu Abbanki yasamu damar had'a kan mijinkine, ya ina jinjinama fik'irarki ke da munubiya kuma zaki 6ata shirin, karma ki bari 'Yar uwarki taji maganar zubda cikinnan, wlhy zaku samu Matsala ne babu ruwana”. Munaya ta share hawayenta, “shikenan Aunty Salamah nabar maganar insha ALLAH. Amma a yaran nan masu mana aiki bak'ya tsoron wani yaci amanarmu?”. “komai zai iya faruwa, domin amana tayi k'aranci a rayuwa, tunda yau gashi Harun yafito cikin masu cin dunduniyar Galadima, amma ki kwantar da hankalinki, su duka ukunnan da kike gani amintattunane, kuma Saleem ya saka mana idanu sosai a kansu”. “to Alhmdllh aunty, ALLAH kamana jagora”. “amin dai, saikima Munubiya dukkan bayanin da mukayi, ki bata itama ta gani, zuwa gobe zan aiko Bilkisu ta kar6a min, kuma ki fad'a mata yakamata ta koma gidan ta, dan gaskiya aiki bazai cigaba da yuwuwaba tana gidannan, saboda kinga ba ita kad'ai baceba, yanzu haka randa zaku zo da zamu kama Muftahu wlhy nasha wahala wajen nemanta naji kokin iso? dan ta tabbatar min inhar kin iso k'asarnan saitaji a jikinta, amma naita kiranta batayi picking ba, ashe wai wayar na hannun Feena”. murmushi nayi nace, “sorry sweet auntynmu, insha ALLAH zata koma gobe”. “shikenan, bara na wuce to”. “to Aunty ngd sosai, ALLAH ya bada ladan zuminci, ammafa gaskiya kinci zalin muftahu da yawa”. Dariya tayi sosai, “kibari kawai, nima wlhy ina marinsa tausayinsa Na ratsani, insha ALLAH zan nemi yafiyarsa zuwa nan gaba, ALLAH yasa ya yafemin dai”. “hhhh zai yafe miki aunty ai duk cikin aikine”. Mun rakota har tsakar gida, su Munubiya na tsokanarmu wai nad'an sammusu sirrin suma. Daga ni har aunty Salamah dariya mukayi kawai. Bayan dawowarmu na turama Munubiya massage akan taje tagani itama. Sai da taja wasu times sannan tamik'e tana fad'in bara tad'an watsa ruwa. duk muka amsa da to saita fito. ************************** Su Abba sun isa lafiya, anzo da motar Ambulance d'in asibiti aka d'auki Abba, yayinda Sauban da baba k'arami da inna khumar yazo d'aukarsu su kuma. Inna da baba k'arami sai baza ido suke suna kallon gari. Gida suka wuce kai tsaye, yayinda aka wuce da Abba hospital shikuma. Sun iske jakadiya a gidan, dandanan aka shirya musu abinci, itadai inna sai jinjina k'yawun wannan gida take, yanzu anan gidan jininta ta rayu?. shi kansa baba k'arami ya yaba, Yakuma k'ara tabbatar da manyan k'asarmu Na hutawarsu. ************************** Babu yanda Muftahu baiyiba dan ya sarrafa agogon hannunsa amma hakan ya gagara, Dan bak'aramin d'auri ya shaba. Kusan gab da magriba Wanda ke kawo masa abinci ya shigo, ajiye kular abincin yayi sannan ya matsa kusada muftahu zai kwanceshi, cikin murya k'asa-k'asa kamar mai rad'a yace “yalla6ai inhar zaka biyani wlhy zan ku6tar dakai”. Kallonsa Muftahu yayi sosai nawasu mintuna, “ka tabbatar?”. “wlhy Oga da gaske nakeyi, Dan wannan matar da kake gani bata wasa bace, duk abinda ta fad'a zata iya aikatashi wlhy”. Murmushi Muftahu yayi, yace, “nawa kake buk'atar Na baka?”. “tab aini Oga dubu 100 ma ta wadatar”. Muftahu yakuma Murmusawa, “zan baka 200”. Da sauri yaron yaja baya cikin razana, “oga dubu 200 fa? Yo ai sai a d'auka nafara yankan kaine”. Sosai abin yabama Muftahu dariya, Dan haka ya dara, yo dubu 200 a wajensa ai bata wuce ta siyen agogo ko takalma ba, amma shine shi yake ganin 200k a matsayin wasu kud'in da har za'a iya d'auka yayi yankan kai. Kallonsa yayi yana murmushi, “karka damu to, amaimakon nabaka kud'in a hannu a zargeka mizai hana Na bud'e maka wata Sana'a da zakabar wannan aikin da kakeyi yanzu”. “to ai Oga karkaje kasa a kamani wataran, nikuma inhar zan samu Sana'a to zan nutsu”. “haba abokina, ya zakamin rana nikuma Na maka dare, karka damu kaidai ka aminta dani kawai”. “to Na amince, yau sai k'arfe 11 zan kawo maka abincin dare, a time d'in sauran sun fita club, insha ALLAH nikuma zan dawo baya nace Na manta da abincinka, daga nan saina ku6tar dakai, sukuma na sanar dasu Na dawo ban gankaba”. “shikenan babu damuwa, idan zaka dawo kazo da account number, dana koma zan maka transfer insha ALLAH”. “to Oga Na gode sosai”. Ya fad'a cike da d'oki. Murmushi kawai Muftahu yayi. “yauwa Oga bara Na kwanceka kaci abincin to”. Girgiza kai Muftahu yayi, yace, “a'a ka barsa kawai, banajin ci, in kanaso d'auka kaci kawai”.. “amma Oga ai.......”. Kai Muftahu ya girgiza masa alamar karyace komai. Shiru yaron yayi ya d'auki kular ya fice kawai, Muftahu kuma ya bishi da kallo. ************************** Har akayi isha'i Galadima yana birnin gayu, saida aka kira sallar magriba ne yafita zuwa massalacin dake plaza d'in yay salla tare da ma'aikatan wajen masu salla, daga nan ya gaggaisa da makwaftan wajen dakan zo masallacin yin salla suma, bai fitoba saida akayi sallar isha'i. daga nan yacema saleem yaje dasu Aryaan su za6i dukkan abinda sukeso ya mik'a mass ATM d'insa, shikuma ya kuma shiga office ya kulle kansa ya d'ora tunaninsa daga inda ya tsaya. Ya dad'e yana zagaye office d'in, yayinda zuciyarsa ke k'ulawa da kwancewa, agogon hannunsa ya kalla, ganin time yayi nisa yasashi furzar da huci, kayansa ya tattaro ya fito, dogaransa duk suka mik'e, suna gaisheshi, amsawa ya shigayi tamkar baya so. d'aya aciki yace, “zamu tafine ranka ya dad'e?”. Kansa ya jinjina masa alamar eh, sannan yace “ama saleem magana”. Da sauri suka amsa da to. Ficewa yayi, sauran dogaran sukabi bayansa. Mota aka bud'e masa ya shiga, za'a rufe murfin ya hana, idonsa akan k'ofar plaza d'in harsu Aiyaan suka fito tare da saleem, dogarai biyu d'auke da manyan ledoji. Suna hangoshi suka k'arasa da gudu, murmushi yayi ya d'aukesu d'ai-d'ai da kansa ya saka a motar, sannan aka rufe musu k'ofar. Sudai dogaransa sai mamakin yanda yake sakema su Aryaan sukeyi. Har sun fara tafiya ya fad'ama sarkin mota suje zasu taho da Munaya. A ladabce sarkin mota ya amsa da to. ***************** Muna tsaka da hirarmu aka kira wayata, sharewa nayi tamkar bazan amsaba, Munubiya ta harareni, ramawa nayi nima sannan Na d'aga. Ciki-ciki nayi sallama, ya amsa daga can, mamaki ya kamani danjin muryar Galadima, katseni yayi da fad'in “ki fito”. Bai jira cewata ba ya yanke wayar. Kamar zanyi kuka haka naji, Yaa Marwan ya fito daga d'aki yana saka rigarsa, kallona yayi yana fad'in “k ba jiranki akeba ne?”. Sai da Na kumbura baki sannan Na mik'e. shikuma ya fice. Da taimakon feena Na had'a komaina, har abubuwan da mama Rabi'a ta bani, sannan suka rakoni. Mun iske Yaa marwan tsaye jikin motan ya dafa k'ofar suna magana da Galadima dake ciki bai fitoba. Dogari d'aya ya zagaya ya bud'emin, ido muka had'a da Galadima Na janye da sauri, shima janyewa yay ya maida hankalinsa ga Yaa marwan dake masa magana. Mamaki ya kamani ganin su Aiyaan, suma cikeda d'oki suka fad'amin a jiki suna dariya da fad'in “Auntynmu!”. Juyowa Galadima yay yana kallonmu, shima Yaa marwan yay dariya kawai, sannan ya rufe mana murfin yanama Galadima sai da safe. Su Aryaan sun kacame da bani labari, yayinda nikuma naketa musu dariya da biye musu, mamaki ya kama Galadima, bai ta6a tunanin ina magana hakaba, ya lafe jikin seat yana kallonmu cikeda birgewa. Nikam nama manta ko gaisheshi banyiba, saida yay gyaran murya sannan Na d'ago Na kallesa, murmushi namasa ina fad'in “yalla6ai barka da dare”. Shima wani miskilin murmushi ya min yana d'agamin hannu batareda yayi magana ba. Aiyaan yay saurin fad'a “auntynmu bafa yalla6ai sunansa ba, sunansa Uncle”. Kamar zan harari yaron sai kuma nad'an murmusa ina kallon Galadima dake kallonmu shima. janye idona nayi daga gareshi Na cema Aryaan to naji zanke fad'a. Har muka kai gida basu barmu mun hutaba, sai surutu suke da bani labarin abinda yafaru a gida bana nan, danaji zasu kauce hanya kuma sainai saurin waskewa. ★★*★*★★*★*★★ Sarkin mota yana ajiye su munaya ya duba gefen seat d'in data zauna, takarda ya gani ya d'auka, dan sanda zasu shige tamasa wata inkiya da hannu. Dubawa yay yaga mita rubuta. Sallama yayma sauran 'yan uwansa sallama akan zai shiga gida. Daga nan ba gidan ya shigaba, saiyay dabarar da yabar masarautar gaba d'aya. Sun had'u da Saleem a inda suka shirya, saleem Ya bama sarkin mota handkerchief d'in da zasu shak'ama Muftahu. Sarkin mota ma yaje ya bama Ameer ne, daga nan ya dawo k'ofar fada amma k'aramar k'ofa tacan baya inda keda k'arancin tsaro. Agaban idonsa su Ameer suka sauke Muftahu a mashin yana cikin yanayin barci saboda abinda suka shak'a masa, saida ya tabbatar sunbar wajen sannan shima ya koma ciki. Yau dai kam ni kad'ai Na kwanta a d'akina, Galadima ko lek'e bai lek'oba, yana can tare da su Aiyaan a d'akinsa. Nima kawai saina kira Momma mukasha hirarmu, tana bani labarin yanda jikin Abie yaketa k'yau a tsakaninnan, dukda kar yanzu maganar bata fita amma yakanyi bamai tsawoba, naji dad'i sosai, na masa addau'a mai tsawo tareda fatan alkairi, daga nan muka cigaba da tattaunawa akan maganar Abbana, da zancen su innarmu dasuka k'i yarda su zauna a gidan, innarmu ta dage bazata zaunaba tunda muma anan muke, saida Momma ta saka baki da mata bayanin da zata gamsu sannan ta amince zata zauna. Nasha dariya, dan dama nasan za'ayi hakan, innarmu kawai kunya da kawaici. Daga nan har muka dawo kan ta Muftahu, dayake tasan komai a kai, da taimakonta nima nake samun k'arfin gwuywa. Itama tasha mamakin jin Harun a lamarin, ta dad'e tana jinjina maganar nan. ta bama Samha muka d'ora da hira, saida naga time yaja ga zazza6in fama ya rufeni, sallama mukayi nai addu'a Na kwanta. Masu iya magana since sabo tirken wawa, saina kasa barcin, naji kawai ina kewar Galadima. Shima kansa yanacan sai juye-juye yakeyi, yakasa barci, bayan sun gama hirarsu dasu Aryaan yay musu shirin barci da kansa suka kwanta, aiki yad'an ta6a yana Neman dabaru akan binciko Muftahu, baiwani dad'eba ya kwanta shima, amma saiya kasa barci, juye-juye yaytayi agadon, ganindai da gaske ya kasa barcinne saiya mik'e yana jan guntun tsaki, kwanciya ya gyarama su Aryaan ya lullu6esu da bargo sannan ya fito da nufin wai zai duba munaya 🤣😜. Jin shigowarsa yasani k'ara lafewa tamkar nayi barci, ya kunna fitilar d'akin yana kallona, yaja wani dogon lokaci sannan ya kashe ya tako zuwa gadon, “nasan idonki biyu ai, dama kin tashi kinbar wani kumshe-kumshe”. Shiru nayi nakumak'i motsawa. Kwanciya yayi a gefena, yaja bargon shima ya lullu6a, tareda juyamin baya, yace “miya hanaki barcine?”. “farkawa nayi”. Na fad'a batareda ba kalleshi ba. Murmushi yayi yana fad'inn “ Hummm”. Daga nan duk mukayi shiru nawani lokaci, kamar an matse bakina nace “yalla6ai na tambayeka please? ”. Yace, “Uhmm”. Juyowa nayi ina fuskantar bayansa, a nutse nace, “wai dan ALLAH ina sauran matan Abie yanzu?”. Da sauri naga ya juyo gareni, ni harma tsoro ya kamani nai baya da sauri, nazata makeni zaiyi, amma sainaji ba hakaba, yace “Munaya mi kika sani a kaina ne?”. “yalla6ai kamarya mina sani a kanka? daga tambaya?”. Yace, “Humm yana matsowa gareni, zan matsa ya rik'o hannuna................✍🏼 Kuyi manage da wannan please🤦🏻‍♀ *_ALLAH ya gafartama mahaifanmu😭🙏🏻_* *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣4⃣ ................Yanda ya rik'e hannun yasani fad'in “please yalla6ai akwai zafi fa”. Sassauta rik'on yayi, ya sauke ajiyar zuciya, muryarshi a sanyaye yace, “Miyasa kikeson 6oyemin abinda kika Sani? shin bak'ya tausayinane? kullum cikin aiki kwakwalwa ta take, aikin Neman kud'in da zan taimaki kaina da ahalina, aiki akan mak'iyana, ya kike tunani a kaina? yanzu haka ji nake tamkar kwalwar kaina zata tarwatse saboda damuwa da abubuwan da suka sakata matuk'ar nauyi, ta6a kiji yanda zuciyata takoma bugawa a slowly”. ya kamo hannuna ya d'ora a k'irjinsa, saitin zuciyarsa. da gaskiyarsa kad'an-kad'an zuciyarsa ke aiki, ba kamar kowanne bugun zuciya dake tafiya normal ba. Sai naji tausayinsa ya kamani, cikin sanyin murya nima nace, “yalla6ai kayi hak'uri da abinda zan fad'a maka, inhar ka kawoni gidanka ne domin muyi aiki tare a matsayin Friend bai kamata ace ka gaza yarda daniba akan sirrinka. kasan minene yake saka kwalwarka da zuciyarka wannan nauyin kuwa?”. Kansa ya girgiza mini. Na gyara kwanciyata ina kallon p.o.p, “Matsalarka d'ayace baka yarda da kowa ba sai kanka, mu cire Momma da papi, dansu aiyukansu sunkai amusu uzuri, Momma hankalinta akan jiyya yake, dan haka kana k'ara mata damuwa, papi kuma babbane shawara da dabarun manya kawai kake buk'ata daga garesa. Sai kuma Muftahu da Harun nakula suma kakan d'an saki jiki dasu akan wasu abubuwan, to amma fa.........”. Saitayi shiru bata k'arasaba. Ya matso jikinta sosai, tare da d'ora hannunsa saman cikinta, murya k'asa-k'asa yace, “Harun da Muftahu amma fa mi? Please ki k'arasa mana”. Kad'an Na juyo nad'an kallesa, Na d'ora hannuna nima akan nasa daya d'ora akan cikina. Janye fuskata nayi Na koma kallon p.o.p d'in. “kayi hak'uri da abinda nake fad'a, badan ina zarginsu bane zan fad'a d'in, dama zancene Harun da Muftahu kuma kamar bai kamata 100% susan komaiba, dan za'a iya sayensu ko tursasasu suci dunduniyarka. domin koba komai har yanzu bakada tabbas d'in cewar babu hannun wasu a cikin masarautar nan. amma kayi hak'uri idan na shiga hurumin daba nawaba”. Shiru yay baice komaiba tsawon lokaci, har nayi zaton nayi laifi ko yayi barci, a sanyaye nakuma fad'in “please & please kamin afuwa yalla6ai”. “is okay”. ‘kawai ya fad'a yana kuma sakani a jikinsa, tareda d'ora ha6arsa saman kaina. Babu Wanda yasake magana a tsakaninmu, kowa yay shiru yana k'ullawa da kwancewa, har dai barci yafara fisgata. “Kina ganin su Aiyaan bazasuyi kuka ba idan suka farka sukaga su kad'aine?”. Naji maganarsa cikin kunnena. “a'a” na fad'a ina girgiza masa kai, “ko'a gida sukad'ai suke kwana dama”. “okay”. Saikuma muka kuma yin shiru, har barci yakuma fara d'aukata yakuma fad'in “kozaki sha Magani ne?”. ‘yay maganar yana ta6a gefen wuyana’. Kaina Na girgiza masa batareda nace uffanba. shima bai sake cewa komaiba.. Yanda numfashina ke sauka a hankali sai ya fahimci nayi barci, shiko gaba d'aya yakasa nasa barcin, tunanin wani Abu daya ta6a faruwa a baya ya fad'o masa, dukda shi ba yayi imani da hakan baneba. 👇🏻 *_Wata ranar juma'a a India, sai suka tashi da matsananciyar damuwar motsawar ciwon Abie, a time d'in ma sun zata rai zaiyi halinsa, hankalin Galadima ya tashi har ciwonsa shima yakai ga motsawa, amma yak'i yarda doctors su dubashi, yace abarsa kawai gara ya mutu ya huta, hankalinsu momma ya tashi, amma Galadima yak'i sauraren kowa, daga k'arshema saiya sulale daga asibitin ya fice abinsa, haka yayta tafiya rik'e da k'irjinsa saboda azabar ciwon da zuciyarsa ke masa, mutane sai kallonsa sukeyi, shiko baimasan sunayiba, yayi tafiya mai nisan gaske batareda yasaniba. k'arfinsa da kuzarinsa sukai gazawar da bazai iya cigaba da tafiyanba, shine yazube a wajen ya fad'i._* *_bai tashi farkawa ba sai awani d'aki mai kama dana bunu, ya yunk'ura zai mik'e amma saiya kasa, wani tsoho ba indiye, a cikin indiyawan ma irin masu k'yawunnan sosai, ya dafa kafad'arsa, cikin harshensu yace ma Galadima “koma ka kwanta d'an saurayi, bakada lafiyane”. Galadima yace “kayi hak'uri baba gida zanje nasamu sauk'i, zamana annan bak'aramin tashin hankali bane ga ahalina”. tsohon yay murmushinsu Na manya, yace “zakaje gida d'ana, ni da kainama zan kaika, amma lallai kai acikin al'amuranka akwai abubuwan ban mamaki da al'ajabi, gakuma tsantsar rud'ani, saidai komai yanada lokacinsa, kuma lokaci zai tabbatar maka hakan, albishir d'aya zanmaka, nanda wasu shekaru dabasu Gaza 7 ba mai taimakonka zatazo, kwarai zatazo gareka, ba lallaine ka fahimci abinda nake fad'aba ko yarda dani, Dan Na lura kaid'in musulmine, kuma bad'an wannan k'asarba, amma wannan mai taimakon naka itace zata zama fitilar haska maka hanya kakai ga cinmma burinka, domin taurarinta da naka sunada matuk'ar k'arfi, harma suna gogayya da juna, zaku zama sh........”. Saikuma yayi shiru yana murmushi, ya shafa kan Galadima yana fad'in “tarin Albarka sucigaba da baibaye rayuwarka data zuri'arka”._* *_daga wannan maganar sai barci mai nauyi ya kwashe Galadima, koda ya farka saiya gansa a asibiti tareda su Momma, yata tambayarsu INA tsohon yake sukace su basu San wani tsohoba, wasu samarine su biyu suka kawoshi asibitin, wai sungansa yafad'i a gefen hanya, zancen tsohon yata damun Galadima a time d'in har yayta bincike kozai gansa amma ko alamun mai kamarsa bai ta6a ganiba, daga hakama saiya cire abin a ransa yacigaba da harkokinsa._* Ajiyar zuciya ya sauke, tareda kuma rungume Munaya, a kan la66ansa ya furta “ALLAH kaine mafi sani”. daga haka yay shiru tareda lumshe idanunsa, barcine yayta fusgarsa harya samu nasarar sacesa. Can gabannin asuba yay wani mafarkin daya sakashi farkawa a firgice, har itama Munaya ta farka tana tambayarsa lafiya?. Kansa ya dafe, da hannu yaymin nuni na bashi ruwa. Sauka nayi daga gadon dan zazzza6inna ya fara hucewa nima, freight na bud'e na d'akko masa ruwa, na had'o da Kofi, zama nayi kusa dashi a gefen gadon na tsiyaya ruwan a Kofi na mik'a masa. kar6a yayi ya shanye, ya mik'o min kofin, zan kar6a ya girgiza min kai tare da min nuni da in k'ara masa. Kuma tsiyaya masa nayi, yakai rabi ya d'aga min hannu alamar ya Isa, bayan yakuma shanyewa ya mik'a min kofin yana fad'in “Thanks”. Kar6ar kofin nayi, ba tareda na tashiba nace “Yalla6ai lafiya kuwa”.. “Mafarki”. ‘yafad'a yana komawa ya kwanta’. Idanu kawai Na zuba masa, kusan 4minutes ya juyo da kansa ya kalleni, “kizo ki kwanta mana”. K'aramar ajiyar zuciya kawai Na sauke Na mik'e, Na d'ora ruwan da Kofi a dirowan gefen gadon na koma inda nake na kwanta. Ganin ya sauya hannun da yay mafarkin kuma yana addu'a sai ban sake cewa komaiba, na kwanta shiru ina sak'e-sak'e a raina mafarkin mi yayi to? da har yasakashi firgita irin haka?. banida mai bani amsa dan haka nayi shiru. Saiya zamto da asuba na rigashi tashi, harma saida nayi alwala sannan na tadashi, da k'yar ya iya tashi yana dafe kai, binsa nayi da kallo kawai harya shige toilet. Lokacin daya fito na fara salla, dan haka saiya fice kawai. A mamakinsa saiya iske Aiyaan da Aryaan sun tashi suna alwala, hakan ya Burgesa sosai. Sai kawai ya kama hannunsu suka tafi massalaci. Bayan an idar da salla bai yarda sun had'u da Sarki ba, ya gudo. Sai dai abinda bai saniba shi Sarki ya gansa, dan yau ya makara salla shima. Wajen Around 9am nagama gyaran d'aki nayi wanka, saina d'an fito falon domin duba dubawa, natarar sabbin kuyangina suma komai sun gyarashi k'al, harma da mana break fast, banyi yunk'urin bud'ewa ba ma balle tunanin son ci, dukda kuwa natashi da yunwa, to amma Momma ta gargad'eni sosai akan cin abinci wani a masarautar, dan haka na fito daga kitchen d'in kawai. Tunkan na shigo nake jiyo maganarsu Aryaan, zaune na iske Galadima su Aiyaan na kusa dashi suna bashi labari, anmusu wanka tsaf, sunsha sabbin kaya iri d'aya. Har yanzu Galadima bayada walwala, na zauna ina gaisheshi, batareda yabar latsa wayarba ya amsa min, su Aiyaan suka dawo kusa dani suna gaisheni, kumatunsu naja ina murmushi, “oh my guys kunsha k'yau, waya muku wanka haka?”.. Atare suka amsa min da fad'in “Uncle ne, kuma ya saka mana tirare yanda kuke mana”. Murmushi nayi, na saci kallon Galadima da yay biris damu kamar baya d'akin, alhalin sanda na shigo na iske suna hira shidasu 'yan 2. Sallamar da wata baiwa keta kwad'awa na amsa, sannan na mik'e na fita dannaji minene? A k'ofar falona na isketa, nace, “miya farune?”. Duk'ewa tayi ta gaisheni, sannan ta mik'omin ledojin hannunta tana sanarmin Sarkin motane yace “na kawo wannan ranki ya dad'e”. Kar6a nayi, na koma ciki. Ajiye ledojin nayi a gabansa, “gashi wai inji sarkin mota”. Idanunsa ya d'ago ya kalleni, yace, “breakfast d'inku ne”. Tashi yay ya fita yana fad'in na shirya zaije ya dawo mu shiga cikin gida gaida mutane. Na amsa masa da to. ___________________ Tun a daren jiya wasu bayi sukaga Muftahu, dan haka suka shiga ihu, dandanan sauran bayin dake kusa da wajan suka firfito, manyan bayin cikinsu ne suka kai maganar cikin gida, shine akasakasu d'aukar Muftahu su shiga dashi. Lamarin yabama kowa mamaki, babu wani mummunan rauni a jikinsa, inbanda d'an jini dake gefen bakinsa, saidai sun sami kwanciyar hankali ganin yana numfashi. Maganar dawowar Muftahu bata baje masarautar ba sai washe gari. Bayan Galadima ya fito daga sashensa zaije fada yaji anata k'ananun magana akan dawowar Muftahu, saidai kuma miskilancinsa bai barsa ya tambayi kowaba ya nufi Fada. Ya isa mai martaba baikai ga isowa ba, dan haka suka gaisa da 'yan majilissar Sarki dake fadar, sannan ya nemi mazauninsa dake gefen Sarki Na dama ya zauna. Zamansa baifi da mintuna 10 ba Mai martaba ya iso, gaba d'aya suka mik'e tsaye, dogaran Sarki sunata kirari da fad'in gyara kintsi da k'yau, duksun baza riguna ba'a gani mai martaba, basu bar kowa ya gansa ba har saida ya zauna a kujerarsa. Baya suka mammatsa mai martaba ya bayyana, atare su Galadima suka rissinar dakai alamun girmamawa, sannan kowa yafito tsakkiyar fada ya mik'a gaisuwarsa ga Sarki, yayinda fadawa ke faman amsawa, tsakanin Sarki dasu kuwa shine d'aga hannu. Mai martaba yayi mamakin ganin Galadima yau azaman fada, bawai baya zaman bane, sai dai yakan dad'e bai zaunaba, an masa uzurine kasancewar ansan ba zaune yake dindin dinba, kuma idan yazo akwai harkokinsa Na kasuwanci da yakeyi, sai dai dolene yakan shigo yayi gaisuwa. Bayan fada ta nutsu aka fara fadanci. K'a idane fadar gagara badau takanyi fadancine a sati sau hud'u kawai, litinin ba'a zaman fada, domin ranace da ake tunawa da abinda ya faru ga tsohon Sarki mahaifin Galadima, talata, laraba, alhamis, asabar, sune ranakun da ake fadanci, ranar juma'a ma ba'ayi saboda muhimmancin ranar ga al'ummar musulmi. A wad'annan ranakun akanyi zamanne daga 10am zuwa 12:30pm, da an tafi sallar zuhur ba'a dawowa, idan kaga anwuce wannan time d'in a fada to tabbas akwai abinda ya farune. A wannan zaman fadancine maganar dawowar Muftahu ta fito, sun tattauna akai harda shirin kuma d'aukar matakai Na tsaro a masarautar. Bayan anyi sallar zuhur ne Sarki ya shige gida, sauran fadawa ma kowa ya kama gabansa, Galadima bai shiga gidaba saiya nufi sashen su Muftahu domin dubashi. Bayan an masa iso ya shiga, ya iske mahaifiyar Muftahu da 'yan uwansa zagaye dashi, har yanzu kuma yana cikin yanayin barci. Ya jajanta musu, Yakuma kwantarma da mamansu Muftahu hankali, kusan mintunsa talatin ya fito ya koma sashensa. Ya iske su Aiyaan kawai a falon Munaya suna kallo, suka taso da gudunsu suka rungumesa, fuskarsa cikeda fara'a ya tarbesu, ya tambayesu ina Auntynsu?. A tare suka bashi amsa, “Uncle tana d'aki ta kwanta kuma tace karmu tadata, inba hakaba jiki magayi”. Murmushi yayi yaja kumatunsu, “kuce zatayi zana kenan idan aka tada ita?”. Nanma atare suka amsa da “eh Uncle, kasanfa Aunty Munaya tacika fad'a, gidanmu tsoron masifarta akeyi, amma ita Aunty Munubiya babu ruwanta”. Galadima yace, “da gaske?”. “ALLAH kuwa Uncle, idanfa mukayi rashinji ita ke zanemu ba innarmu ba, kuma dukanta da zafi, gashi taita hararmu da katun-k'atun idanunta nan”. Sosai abin yabama galadima dariya, dan haka ya dara sosai abinsa yana fad'in, “kubari tajiku to, idan ta zaneku babu ruwana nidai, kunga bara naje naga kota tashi, karfa Ku shigo, dan zata iya zaneku”. Sukace “ai bazamu shigoba Uncle”. Yace, “good boys”. Da sallama ya shigo, amma saiya isketa baje a gado tana shak'ar barcinta, yad'an murmusa kafin ya k'arasa ya zauna a bakin gadon saitin fuskarta, yatsunsa biyu yasaka a gefen wuyanta dan yasan da wahala wannan barcin ya kasance na lafiya, aikam jikinta ringim yake da zazza6i, tausayinta ya kamashi, lallai uwa dabance acikin al'umma, Ashe haka sukeshan wala, tundaga d'aukar cikinma zuwa rainonsa, akoma rainon yaro, daganan tarbiyarsa, lallai masu raina mata ko kallonsu masu k'arancin tunani sune masu k'arancin tunanin ai, ya d'an lumshe idanunsa yana cije lips, ganin ta dunk'ule a waje d'aya saiya ja bargo ya lullu6a mata, harya mik'e ya koma ya zauna, risinowa yay kanta a hankali ya mannama goshinta kiss, sannan yamik'e ya fice. Koda ya dawo saiya wuce d'akinsa, yabar su Aiyaan suna kallonsu. Kayan jikinsa ya cire ya kwanta shima, dan yana buk'atar hutawa kona 2hours ne, kwanciyarsa kuwa babu dad'ewa barci ya saceshi. Kiran sallar la'asarne ya tashesu kusan lokaci d'aya, Galadima yatashi da k'yar, a mamakinsa sai yaga Aiyaan da Aryaan kwance a gefensa suma suna barci, murmushi kawai yayi yasako, saida ya watsa ruwa sannan yay shirin tafiya massalaci cikin k'ananun kaya. Harzai fita saiya dawo yashiga wajen Munaya. tana tsaye gaban wardrobe tana neman kaya, da alama wanka tayi, dan daga ita sai towel. Banji sallamarsa ba, saboda shi idan zaiyi magana bayason bud'e baki, ganin batajishiba saiyayi gyaran murya, a tsorace na waigoshi, ganin shine nai saurin saka kayan dana d'akko ina kare k'irjinna da tura baki, bakinsa ya d'an ta6e, sai kuma ya shiga takowa inda nake, duk takun da yayi sai gabanna ya fad'i, na waiga kozan samu nabar wajen ko abinda zan suturta jikinta sosai, amma sainaga babu a kusa, kuma ina jikin wardrobe d'inne sosai ai. ban gama yanke shawara ba ya k'araso daf da ni, kuma matsawa nayi na matse jikinna sosai a drowa d'in, shikuma yawani had'e gabas da yamma, wannan ne yakuma sakamin tsoronsa a raina, na zata kowata tsiyarce ta kawoshi. Hannu yasaka ya d'ago da ha6arta muka kalli juna, ya tsareni da idanu yanda nakasa janye nawa cikin nashin, munkai kusan 2minutes a haka, kafin yakumamatsoni sosai, ya kai fuskarsa gab da tawa tamkar zai had'e bakinmu, dan haka saina lumshe idanu, murmushi yayi ya hura mata iska akan idanun, ta rumtse idon sosai, ya d'an ja baya yana ta6e baki, kafin yasaka hannu ya cire nata dataketa faman kare k'irji da kayanta, still ya kuma matsawar saitin kunnenta yana fad'in “wane darene jemage bai ganiba yalla6iya”. ‘ya k'are maganar da shafa kirjina ya fice abinsa. Kad'an yarage namasa ihu wlhy, aiko yana fita na durk'ushe a wajen ina sauke numfashi, sometimes nakan rasa yazan fassara Galadima da ayyukansa. Da k'yar Na iya tashi nayi sallar nakoma kan gado Na kwanta. Galadima kam daya fita dariya ce taita cinsa, ya kula Munaya akwai tsoro, kuma haryanzu a tsorace take dashi, cikinnan ne kawai kanci galaba akanta yake samunta cikin sauk'i, ya girgiza kansa kawai yana murmushi. Bayan ya dawo massalaci d'akin nata ya dawo, dan yanason suje su gaida jama'ar gidan, maybe gobe suje masarautar papi ma. A kwance ya iskeni, nak'i kallonsa, jingina yay da mirror yana fad'in “yaya jikin naki?”. Ban kalleshinba nace, “da sauk'i”. “ALLAH ya k'ara sauki, idan zaki iya tashi ki shirya muje cikin gida, kafin waccan tsohuwar tafarama mutane surutu”. “to” nafad'a ina mik'ewa, Na sakko a gadon, harna nufi wardrobe zan d'auki alk'yabba saina tsaya, batareda Na kalleshi ba nace, “toka fita Na shirya”. Hard'e hannayensa yayi a k'irji yana fad'in “ashe bazaki shirya d'inba, dan bazanje ko inaba”. “karkaje d'in, ai akwai bayi” nayi maganar a zuciyata. Kayan Na d'auka na shiga toilet, shikuma ya ta6e baki. Babu dad'ewa na fito tsaf, nayi k'yau, nazo ta gefensa na d'auki turare nasaka kad'an sannan na kallesa nace, “na shirya”. Baice komaiba ya nunamin hanya, gaba nayi yana bina a baya muka fice. Kasancewar tazarar dake d'an tsakaninmu da sassan nasu muka shiga mota, dan banajin dad'in jikinna, bama zan iya tafiyarba. 6angaren Abba hayatudden muka fara zuwa, daga nan sai sashen matan mai martaba, soyayyar da uwargidansa ke nunamin yasani k'ara k'aunarta, sai addu'a take zabgamin akan ALLAH ya saukeni lafiya. Galadima kad'ai ke amsawa, amma ni saidai a zuciya kawai. daga nan muka d'an shishshiga wasu sassa, 6angaren mama fulani shine k'arshen zuwanmu. Kunsan dai mutuniyar taku akan mulki, tana kishingid'e kuyanginta nata bauta, mai matsa kafa daban mai firfita daban, ga masu bata labarai, tufa takeci cikeda k'asaita da izza. Amintacciyar baiwarta data mana iso tana gaba muna biye, mama Fulani ta d'agama kuyanginta hannu alamar subata waje. Rige-rigen ficewa suka, yayinda mukuma muka k'arasa gareta, idonta a kammu ko k'yaftawa batayi, nidai tsarin ALLAH na nema daga sharrinta, ina dalili wannan kallon k'urilla haka?. Galadima yace, “barka da yammaci”. nima saurin fad'a nayi. A yatsine ta amsa mana, ta d'ora da fad'in “Saraki kayi wuyar gani?”. Galadima ya murmusa yana kallona, “Ranki ya dad'e kinsan mai amarya ai yafi dubu wahalar gani dama”. “Humm” kawai tace batareda ta amsaba. Sai zuwa can tace “nafa manta, ina tayaku murnar samun k'aruwa”. “mun gode ranki ya dad'e, amma taki murnar itace tazo a latti, gashi kuma idonkine yafara hango abin cikin kwan tun a india”. Mama Fulani ta tsatstsare Galadima da idanu, shikuma yay salute nata yana murmushi. Jitai kamar zata makesa dan haushi. Ya lura da haushin da taji, dan haka ya kama hannuna muka mik'e tsaye yana fad'in, “bara mukoma inda muka fito ranki ya dad'e, a huta lafiya”. Bai jira amsartaba mukayi fitowarmu. Da kallo kawai ta bimu, takasa koda motsawa, tarasa miyyasa yau Galadima da matarsa suka mata wani mugun kwarjini? batada mai bata amsar tambayar tata... Yini guda yau Galadima a gida yayishi, baije ko inaba, sai da daddare Nuren yazo sukayi magana, daga nan yace ya nema mana tickets d'in zuwa masarautarsu. Washe gari muka tashi da shirin tafiya masarautar su papi, mukad'ai muka tafi, babu kuyangi babu dogarai, dagani sai shi dasu Aiyaan, sai Nuren..................✍🏼 *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu_*😭🙏🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS. ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣5⃣ ...................Abin yabani mamaki ganin yanda akazo tarbarmu, yo saikace wani Sarki, hakan yakuma tabbatarmin da Galadima d'an gatane a wannan masarautar. A masarautar ma gungun mutane muka iske wai masu tarbarmu, ni dukma sai kunya ta kamani wlhy, musamman da Mom ta rungumeni tana fad'in “ga maman twins d'inmu ga Maman twins d'inmu”. Galadima dai murmushi yayi, Nuren kam dariya ya kemin. Lallai naga tsantsar soyayya a wannan masarauta, sai nan nan ake dani kamar wata sarauniya, duk wani Motsina Inno tace minakeso? hakama mom. Aiyaan da Aryaan kam ai suna tare da Galadima, duk inda yasaka k'afa suna biye. Nikam dai a kwana biyun da mukayi babu abinda zance da wad'annan bayin ALLAH sai godiya, naga karamci naga hallaci sosai, hakama k'annena. Sosai Galadima yasamu tattaunawa da papi a tsakaninnan, sunyi maganganu masu muhimmancin gaske. Musamman akan ciwon Abie da cikin jikin Munaya, harma da Abbanta. sosai kuma Galadima yakuma samun haske akan lamuran. Kwannamu biyu muka dawo cikeda kewarsu, tare da tarin alkairi ga wad'annan mutane masu tsayawa a rai. Mun dawo da kwana 1 yaran gidanmu na ma'auri suka kawomin ziyara. Aunty khaleesa, aunty Hauwa'u, aunty Ramlah, aunty Raheenat, matansu ya hameed, Fiddausi, Siyama, Zarah, Safara'u, Fauziyya, Haleematu,Munubiya, Ayusher, Feena. Wayyo dad'i wlhy saika d'auka biki akeyi, rasa inda zansaka kaina nayi saboda dad'i, shi kansa Galadima ya fahimci ina tare da tsantsar farinciki, nima dagewa nayi namusu hidima iya hidima, dan hardani aka shiga kitchen. Sukam duksun rikice da mamaki, dama haka gidan sarautar yake, dan saidama Galadima yaje da kansa ya shigo dasu. Su Aiyaan anata murna anga 'yan gida. Ranar dai anan suka yini zir, dazasu tafi Galadima yay muzu alkairi mai yawa tareda godiya ta musamman. Sunji dad'i sosai kuma sunyi farinciki, sunata masa godiya nima ina tayasu. Da zasu tafi jinai tamkar na rik'esu, aiko harda 'yan kwallana, sauk'inama kawai su Aryaan tare dani. Kowaccensu tatafi da labarin data gumtsawa uwarta a bayan fage, dansu Zarah dai sun Shiga taitayinsu, sun gane ruwa ba sa'an kwando bane, nanfa hassada da bak'inciki tamkar ta babbake zukatansu, mamansu Yaa hameed hardama Abba ALLAH ya Isa tana sharar kwalla, wai yasan da gidan sarautar amma ya yarda Zarah ta auri d'an sanata, ga aunty khaleesa nanma kullum cikin matsala da miji, dan kishiyarta akwai kissa. *_ALLAH yarabamu da ciwon hassada fans_*😏 Sati d'aya da zuwansu muka koma India, saboda Company suna Neman Galadima da gaggawa. harda innaro iya bala'i muka tafi🤣. A jirgi taita kudundune fuska a gyale wai batason ganin tashin jirgi, duk tsare gidan Galadima saida yayi dariya, Aryaan da Aryaan kam sukaita tsokanarta. Yau babu masifarnan dan bata kulasuba, saima Galadima ne ya hanasu. nikam banza na musu dan tawama ta isheni nikam. Jikina sai ciwo yakeyi, ga cikina na mun ciwo shima kad'an-kad'an. Khumar da Sauban da Samha sukazo d'aukarmu, muka rungume juna da samha muna farinciki. Daga nan muka wuce gida, yaukam munashan k'auyancin innaro, ni harma tabani haushi, komai tagani saita tambaya, Kodai su Aiyaan basa abinda takeyi. Mun iske jakadiyane kawai sai bayi, Su Momma da innarmu suna asibiti, Mudai sama muka haye ni da shi, 'yan biyu kuwa suna wajen Samha ta kasa ta tsare, innaro kuma aka barta da jakadiya. Ko ina tsaf yasha gyara tamkar mai d'akin na nan, Muna shiga kwanciya nayi bisa kujera, naja bargon saman gadon na lullu6e, kallona yayi da mamaki “k lafiyarki kuwa?”. “zazza6i”. kawai nace masa na k'udundune har kaina. Zama kawai yayi ya zubamin idanu cike da tausayi, ganin zaman bazai masaba yatashi ya shiga toilet, saida ya gama dukkan uzirinsa sannan nima ya had'amin ruwan wanka, tadani yayi, na tashi da k'yar tamkar zan masa kuka. Yace, “tashi kije kiyi wanka kozakiji dad'i”. Baki na tura masa gaba. “idan bazaki iyaba tashi muje na miki”. ‘yay maganar cike da basarwa’. Harara na zuba masa sannan na mik'e na nufi bayin. shikuma ya ta6e baki yana wani mikilin Murmushi. Abincima sai nan ya saka aka kawomin, dan nakasa sauka. Innaro sai catake wai nacika langyare, dan naga yana shagwa6anine shiyyasa nake ta6ara, ai badaga kaina aka fara cikiba. Galadima dai murmushi kawai yayi danshi lamarin innaro abin dariya ya d'aukesa, tana buk'atar uzuri. Bayan nasamu naci abinci daya bani nasha magani, harzan kwanta a sofa yace na koma saman gadon, kamar zanyi magana saina fasa, na tashi kawai na koma. Yana kammala duk abinda ya dace yafice asibiti domin duba Abie da Abba. Yaji dad'in yanda yaga canji sosai a jikin nasu su duka, dan raunuka da yawa sun warke a jikin Abba, da bakinshi ma ya amsa masa gaisuwa yana masa godiya, inna da baba k'arami sunata saka masa albarka. maganar da abie ya fara kuwa rungumesa yayi yana kuka Abie nayi, hakama su Momma, a hankali Abie yace “ina d'iyata Muh'd”. Murmushi Galadima yayi, yace, “zuwa anjima zaka ganta Abie, yanzu na barta tana barci zazza6i ya rufeta”. Momma da Aunty Mimi sukace “ALLAH dai ya sauketa lafiya to”. Babu kunya Galadima ya amsa da amin. Aunty Mimi dake kusan dashi ta doki gefen hannunsa, “kai mara kunya, shine zaka amsa”. Hannu ya saka ya rufe bakinsa yana fad'in “ni jikan Abdul'fatah da Abubakar”. Dak'uwa Momma tamasa tana kai masa duka, ya matsa da sauri yana dariya. Abie ma murmushi yakeyi, lallai yau yakuma ganin canji tare da d'ansa sanyin idaniyarsa, sukam yaushe rabon da suga irin wannan nutsuwar tare dashi haka, lallai dolene su godema ALLAH da shigowar Munaya cikin rayuwarsa, basu da wani abinda zasu iya biyanta har abadan, saidai suyita mata fatan alkairi da k'yautata rayuwarta. Saida na tashi sannan muka tafi asibitin muma, wajen su momma muka fara zuwa, Momma da aunty Mimi sukazo suka rungumeni tamkar zasu had'iyeni dan dad'i, nikam duk kunyarsu ta gallabeni, sai 6oye fuska nakeyi, koda zan gaida Abie ban yarda na kalleshiba. Sauban da Samha sai dariya sukemin. Duk bak'in halin innaro saida tayi kuka ganin halinda Abie yake ciki, taita kwarara masa addu'a kuwa. Su momma sunji dad'i, kuma sunata girmamata. Samha sai dama-dama takeyi dasu Aiyaan, motsi kad'an tace, “ALLAH yasa Aunty gimbiya muma ta Haifa mana irinku”. Su Momma sunata amsa mata da amin. Nidai kaina na k'asa saboda kunya, ina lura da Galadima kuwa duk sanda tafad'a saiya murmusa kuma bakinsa ya motsa alamar yana amsawa da amin. Sosai naji dad'in ganin jikin Abbanmu shima, dan har magana mukayi, jikinsa yayi k'yau sosai, karayunne ma kawai suka rage nakula, amma k'ananun ciwukan duksun warke, to wajene dayake samun kulawa ta musamman. Munaya harda rungume inna, itako ta tureta tana hararta, su Aiyaan kam duk sun d'are bisa cinyarta suna d'okin ganinta da kewarta. Itama tayi kewarsu over, tsakanin uwa da d'a kenan (iyaye mata ga naku fa🥰🥰🥰❤👍🏻). Haka muka dawo gida ina farinciki, koba komai nasamu nutsuwa mai yawa a yau d'innan, aiko ban yarda mun kwantaba saida nayi nafilfili domin mik'a godiya ta ga ubangijin sammai sannan na kwanta. Galadima kuwa muna shigowa d'akin sirrinsa ya shiga yanata aiki. ___________________________ Hankalin Minister ya kai k'ololuwar tashi shida families nasa akan 6atan 'yarsa, farhat, duk wata hanya daya kamata subi sunbita amma babu koda labarin Wanda ya ganta, tun lamarin nabasu mamaki harya koma basu tsoro, ga wani text massage da akama minister d'in d'in kwana 10 daya wuce. _Idan kana buk'atar 'yarka kana iya mik'a wuya._ Wannan massage ya tsaya masa a rai, har police sun kar6a amma sun gaza gane komai gameda massage d'in ko wannada ya turo shi. Mahaifiyar Farhat harda kwanciya asibiti, dan ita kad'aice mace a gidan, dan haka suke masifar son yarinyar da mata gata, dudu shekarunta 16 ne kawai, tana wata private boarding school ne a abuja. a binciken da Galadima yakeyine ya gano hakan, kuma yayta bibiyar yarinyar har saida yasamu nasarar saka Nuren ya kwamuso masa ita. ___________________________ Tunda muka dawo India bani da lafiya, kullum innaro cikin min gorin ni ragguwace take, bana wani kulata dan tawa ta isheni, koma uwarmi zata fad'a ta shekara fad'i, bazan yarda mu Raba hali a gidan surukai naba, nakan bar lamarinta a wasan jika da kaka agabansu, amma ni nasan badan hakan takeyimin ba, ita kanta innarmu bata kulata ko kad'an, idan tanayi shiru take mata ma. Kulawa kam bazanyi butulciba ina samu wajen Galadima dasu Momma, musamman ma jakadiya da Aunty Mimi. Saukina ma cikin bamai tsurfa baneba, komai inaci hankali kwance, kuma ban ta6a amaiba ko wani zubda yawu, saidai zazza6i da ciwon jiki. Yaudai dole Akash yazo har gida ya sakamin k'arin ruwa, kozan sami sasaauci. Yini guda yau a gida Galadima yayisa, duk wani motsina akan idonsane. ************************** *_5 months ago_*🙆🏻🙄😆 A kwana atashi babu wahala wajen ubangiji, rayuwa ta shud'a, kwanaki nata sauri, a wanni da mintuna kam ai ba'a cewa komai, abubuwa masu yawan gaske sun faru a watanni biyar d'innan, ciki harda warkewar Abbanmu sarai, tamkarma baiyiba, saidai k'afarsa da yakan d'an tizgid'a saboda matsala data samu, shima saika k'uramasa I done zaka fahimci hakan. Innaro dai dasu Aiyaan tuni suka koma saboda makaranta, sai dai duk Hutu Galadima yakansa azo dasu Aiyaan d'in, hakama Munubiya da yaa marwan sunzo sun mana sati biyu sukaga jikin Abba da Abie. A wattani biyar d'inna Galadima yaje Nigeria kusan sau hud'u, dukda bai ta6a fad'amin wani abuba ina samun bayanai ga Saleem da sarkin Mota. har yanzu kuma Farhan d'iyar minister tana hannunsa, hakama Malam Saminu driver Alhaji Balala. Yaran gidanmu masu cikkuna duksun haihu, su Siyama an zama iyaye, naji haushin rashin halartar taron suna ko d'aya, dan dana fad'ama Galadima inason zuwa banza yamin, naci kukana kuwa na hak'ura, sai turomin abubuwan da akayi sukaitayi ina gani. Cikina ya fito kwarai da gaske, dan yanzu yana cikin wattani 7 da wasi kwanaki, yamin d'as yakuma sakani k'iba, duk kamannina sun canja, kumatuna sunyi manya, dukdai wanda ya ganni zaisan na canja, hakama Munubiya, idan ta turomin hotonta nata dariya kenan. Tsakanina da Galadima kuwa har yanzu muna a yanda kowa ya sammu, canji d'aya zance ansamu shine nuna yawan tausayinsa akan cikin jikina, dan dukkan wani motsina cikin nuna damuwarsa yake. Idan yana wajen aiki kam yakan kirani sau uku sau hud'u dan yaji lafiyata kawai. A 6angaren iyayensa da danginsa kam banida abin fad'a sai godiyar ALLAH, dan tamkar a kainane aka fara ciki haka suke nunamin kulawa. Hakan nama Innarmu da Abba dad'i, hankalinsu na kuma kwanciya sosai akan aurenmu. baba k'arami yakanyi wata d'aya ya tafi Dady kuma yazo, haka suka dingayi har ALLAH yabama Abba lafiya. Jikin Abie ma said dai muyitama ALLAH godiya, dan bayan magana an kuma samun cigaba 6angaren motsa hannunsa, yanzu kuma maganarsa takan d'an fito yanda akeji, saidai duk wannan cigaban da ake samu babu Wanda yasan dashi, har mai martaba k'aninsa, kaf masarautar gagara badau da dukkan wani makusanci bai San komaiba a kai, dan papi yahana fidda maganar, ko zuwa akai dubashi yakan komane tamkar yanda ya saba kamar da, daga mama Fulani har mai martaba sunzo kusan sau uku dubashi, hakama Muftahu da Harun, 'ya'yan Sarki ma dama suna k'ok'arinzuwa lokaci-lokaci suma. Hakama Hayatuddin Autan mama Fulani. amma babu Wanda aka bama damar sanin wani sirri akan jikin Abie d'in. dagamu sai mu kawai muka Sani. Dukda fama danake da kaina haka na dage muka cigaba da addu'oin nan, zuwan innarmu ma yakuma sakamu ho66asa saboda taimakon da take bamu, sannan muka raba addu'oin ga wasu musulmai malamai dake nan suma suka cigaba da tayamu, aka cigaba da bama Abie yanasha da wanka, doctors d'in sunyi surutunsu harsun gaji sun barmu, dan munk'i fasa masa amfani dasu, tunda muna ganin haske a lamarin sosai. A wata ranar talatar da su Abba suke shirin tafiya k'arshen satinne ina zaune a falo ni kad'ai, dan Galadima ya fita aiki tun safe, zafine ya isheni na dawo falon na k'ure AC, dan Galadima ya saka ma na bedroom d'in key saboda k'urewa da nakeyi, gashi inata fama da mura, shi kansa abin cikina ance tana Neman shafarsa. nikam bana iya hak'uri da Abu mai sanyi konasha ko AC. Sosai na baje ina kwasar dad'ina, sai faman lumshe idanu nake a cikin kujera, gama wayarmu kenan da Munubiya itama tana bani labarin halin son Abu mai sanyin datake a ciki, kullum Yaa marwan fad'a shida mama Rabi'a amma bata d'aga k'afa, data faki ido saita sha, Ayusher da dole ta dawo gidan tayata wasu abubuwan saita gani ta sanarma Yaa marwan, shikuma yay ta jarabar masifa, amma hakan bazai hana gobe tagani ta shaba........ Jinai kawai iskar dake ratsani ta daina shigata, na bud'e ido sai naga Galadima tsaye jikin k'arfen bene daya shigo ta falon ya hard'e hannayensa a k'irji ya zubamin ido ransa a 6ace, hannunsa rik'e da remote d'in ACn. Tsorone ya kama ni, na tashi zaune ina wani marmar da idanu, da hura kumatu danaketa yi, takowa yayi inda nake, idonsa tamkar zai fad'o dan hararata “k kin rainani ko? bazan hanaki Abu sau d'aya ki daina ba, ki duba muran dake damunki tun cikinnan nada wata 3, shin ke bazaki tausayama kanki baneba?”. Shiru nayi bance masa Uffanba, sai faman kumbura baki dai nake yi. “kinsan ALLAH idan baki maida wannan bakinba na kamashi saiyayi jini”. Da Sauri na maida bakina, dan ban manta muguntar da yaminba kwana biyu daya wuce, ba k'aramin morata yakeba yanzu, saboda ALLAH yabani ciki mai sakani yawan buk'ata, sai komai ya lafa nayita masa kuka, shikam ya shareni saboda shegen miskilanci da k'asaita, idan na ishesa yace zai makeni, aibashi yace na kawo kaina ba, dan haka nabar cika masa kunne da ihu, anjima ma nazo yi zaiyi tunda ba fyad'e yaminba ninake kawo kaina. Sometimes nakanji haushin furucinnan nasa, nakuma yi alk'awarin nisantarsa, amma bana iyawa, kona d'auki alwashin saina karya, da yazo yara6u jikina nake mik'a wuya, mugun tunda ya gano lagona saiya dunga bina ta wannan hanyar, duk sanda yaji buk'atata yasan yanda zaiyi ya ra6u da jikina harta kai ga wani abinda nikuma zan mik'a wuya batareda na saniba, saidaga baya nake gane kuskurena. Ganin namasa banza nak'i tankawa saiya shige bedroom yana tsaki, komawa nayi na kwanta ina share hawaye. ga zafi ya fara addabata. Kusan mintuna 19 sannan ya fito, ya canja kayansa zuwa k'ananu, da Alama wanka ma yayi, k'in kallon inda yake nayi harya samu kujera ya zauna, remote ya d'auka ya kunna TV. Haka mukaita zama tamkar wasu kurame, kusan 30minutes, kiran da Nuren yamasane yasakashi d'agawa, bansan miyake fad'a masaba naga dai ya mik'e ya shiga d'akin sirrinsa. Na dad'e ina kallon k'ofar, zuwa can nima na yanke shawarar binsa kawai. Doguwar rigace yellow a jikina, batada hannu, sannan bata kaimin k'asa ba, kad'an ta wuce guywata👗, banason kaya masu nauyi saboda jin zafi, sai silifas d'in k'afata jaa mai taushi. cikinan ya kaimin ko ina, jinake kamar na jawo haihuwar na juyeshi na huta. Ciki-ciki nayi sallama, bai jiniba, hankalinsa nakan Computers d'in d'akin dayake k'ok'arin dai-daitawa, duksun kawo wuta, har k'aton glass d'in dake jikin bango guda na d'akin, ban ta6a d'aukar shima Computer baceba sai yau, dukna d'auka saboda ado aka sakashi a wajen. Sallamar na k'ara yi, ya juyo yana kallona, idonsa na cikin medical glasses mai haske, dan har kwayoyin idanunsa ina hangowa. Kamar zai shareni saikuma ya amsa mini, juyawa yayi yacigaba da abinda yakeyi, mikuma yagani saiya juyo, ya jawo kujera ya gyaramin, yay min alamar da ido na zauna. Babu musu na zauna, ya d'auki remote ya rage gudun AC d'in d'akin, sannan ya juya ga abinda yakeyi. Yanda yake sarrafa Computers d'in saiya tafi da imanina, kai guy d'innan yasan Computer over. Bansan lokacinda bakina ya su6uce nace, “yalla6ai ALLAH ya baka”. Juyowa yayi yana kallona da mamakin furucina, ya saka pen d'in hannunsa a baki yana wasa da shi, kafin ya shiga takowa gareni, k'asa nayi da idanuna nabar kallonsa, yaja kujera ya zauna kusa dani, idonsa a kan cikina, ban Ankara ba naji hannun nasa a saman cikin, idanu Na d'ago Na kallesa, ya d'agamin gira d'aya yana fad'in “ALLAH ya bani k'yautar magaji?”. Murmusawa nayi ina girgiza masa kai, “niba haka nake nufiba fa”. “mikike nufi to?”. ‘yay maganar yana janye hannunsa daga cikin nawa’. Fuska nad'an ya mutse, cikin salon yanga nace, “ina nufin ALLAH yabaka nasibin sarrafa Computer's ”. Yanda nayi maganar cikin salo saiya sakashi murmusawa yana ta6e baki, “toni miye namin yanga yalla6iya? saikace kina tare da masoyinki?”. Haushi ya kamani Na dalla masa harara. Bai kulaniba ya mik'e yana fad'in, “masu cikifa saida uzuri”. Harna yunk'ura zan mik'e yace, “oh haushi kikaji? to sorry zauna kiga wani abu”. Komawa nayi Na zauna INA k'unk'uni. Hotunane da yawa ya nunomin daga cikin Computer, ya danna hoton farko ya fito sosai. Batareda ya kalleni ba yace, “wannan sunansa *Kabiru Ibrahim*, nasanshi shekaru kusan 9 da suka shige a dalilin neman bayanan sirrina tacikin Computer, nabashi dama yashiga sosai saboda a time d'in yaci k'arfina, inada yak'inin wanine yabashi wani yanki sirri daga abinda nake da shi, ganin ya zuk'i bayanai 90 a cikin 100, saina tura masa goman gaba d'aya, saida ya zamana 99 duk sun shige ga Computers d'insa sannan Na nuna masa banbancina da shi, Na lalata abinda yake da shi da Wanda ya samu agareni, tundaga wannan ranar kuma nafara bibiyar rayuwarsa. Abin mamaki saina gano yanada Ubangida, shine wannan, *Timothy yoha*, dukkan abinda ya aikata agareni Umarnin uban gidansane Timothy, Na maida akalar tunanina ga Timo, saina iske shima aiki yakema wani, ba kowa bane face tsohon shugaban k'asarmu *Labaran Ahmad kachia*. shine wannan, nasan kuma k'ila kisansa dukda dai lokacin dayayi shugabanci bana tunanin an haifeki ma gaskiya, ta silar *Former p... Labaran Ahmad Kachia* nasamu wani kundin bayanai akan tsantsar abotar dake tsakaninsu su a k'alla 15, babu maijin sirrinsu saboda Kansu a matuk'ar had'e yake, ALLAH yayima 4 daga cikinsu rasuwa shekarun baya kad'an, saisu 11 suka rage”. Ya kumayin wasu 'yan danne-danne nidai duk ina kallonsa da mamaki, hotunan mutane 15 suka bayyana, sai dai an lik'e fuskar mutum 4 alamun wad'anda suka mutu kenan. Gaban frigate d'in d'akin yaje ya had'a Coffee a mug, sannan ya tako zuwa gareni ya mik'amin, kaina Na girgiza masa alamar a'a, ya d'aga kafad'a sannan ya juya zuwaga Computers d'insa. “wannan mutane hud'un sune jiga-jigan wannan abota, d'aya ya rasu a cikinsu saura uku, *Josaya Bamma* shine mataimakin *Alhaji Lawan tanderu*, bayan mutuwar tanderu shugabancin wannan abota ya dawo hannunsa, dukkan wani shigi da fici na man fetur dake faruwa a Nigeria josaya Bamma yasanta, dan sune masu yinsa, yanda ake fita da mai a k'asar da yanda suka mallaki rijiyoyin mai ba bisa k'a ida ba, gwamnati kuma batada damar magana domin sune masu fad'a aji, sune tsoffin shugabanni da suka San dukkan sirrin k'asar, sai *Bana baba gana*, dukkan wasu magunguna dake shiga Nigeria saida saka hannunsu, akwai wad'anda batareda k'a idaba suke kaita shi da *Alhaji balala* da *William Solomon*, domin manyan likitocine masana sosai, *Hajia A'i Barnawa*, babbar d'iya ga tsohon soja *Garba mai dala sokoto*, tashiga wannan group d'in sanadin k'awarta *Victoria*, dukkan wani cin zarafi mata ko cin dunduniya suke saka ido, kullum suna ik'irarin sune masu Kare hak'in mata a zahiri, amma a bad'ini ba aikin da sukeba kenan, suna aikin gyara aljihunansu ne. wannan shine *Mansur Habibu Abu*, wannan kuma *Abdul-Naseer Nafi'u*, da *Miracle Asun*, wad'annan dukkansu manyan 'yan kasuwa ne, amma a bayyane, amma a 6oye su sukasan tsiyatakun dasuke shiryawa a k'ark'ashin k'asa *Sagir sulaiman Sulaiman* minister mai mulki a yanzu, sai wannan da wannan duk sun mutu banida matsala a yanzu tsakanina dasu, Munaya inason sanin alak'arsu da Mahaifina, wad'annan mutanen, domin sune mahaifina yay zama dasu ana gobe wannan ciwon zai sameshi, a daren ranar kuma Abie yashiga wajen mama Fulani domin gaisheta, jakadiya data masa rakkiya ta tabbatarmin da lallai yafito ransa a 6ace daga wajenta. Sannan a wannan ranar matarsa ta uku ce ta kawana a turakarsa, alhalin kuma kwannan matarsa ta biyuce, amma saboda kud'in data bama jakadiya da dad'in bakinta saita kaita turakar Abie a wannan daren, takuma sanarma matarsa ta biyu cewa takawa bashida lafiya yana fama da mura. kwana biyu kuma kafin faruwar dukkan wad'annan abubuwan Abie yayi zama Na musamman da Hakimansa saboda kama Wazirinsa da yayi Dacin amanar Masarauta wajen d'aukar sirrin cikinta ya bama wasu bak'in turawa da ba'asan dalilinsu na yin hakanba, a bincikena d'aya a cikin turawan ya Mutu, amma d'ayan yana nan da ransa. Abie ya kwanta jiyya da sati biyu aka kashe babban malaminsa, limamin masallacin sarki maikuma bama Abie shawara akan addini. dukkan wad'annan dana ambata miki sunayensu a kwai hotunansu anan d'akin, akwai abokin mahaifinki da kika fad'amin, shine Alhaji Mamman k'afur Wannan babban yaron Alhaji Lawan tanderu ne, dan wannan group sunema suka tsaya masa ya fito takarar shugaban k'asa, babbar matarsa k'anwar matar tanderu ce, wadda a gidan tanderun ta taso tun tana k'arama. Senetor halluru garba abokin Alhaji Mamman k'afur Ne sosai, akwai wani 6oyayyen sirrin dake tsakaninsu kuma, sai dai ban saniba ko Abbanki yasan wani Abu a ciki. Idan nace zan cigaba damiki bayanin sirrikan dake cikin d'akinnan kanki bazai iya d'auka ba Munaya, amma nabaki damar kimin kowace tambaya ni kuma zan baki amsarta batareda shamakiba”. Ajiyar zuciya Na sauke, Dan tabbasa kaina bazai iya d'aukar wannan bayanan nashiba inhar suka wuce zurfin haka, Na yink'ura zan mik'e, saiya matso ya taimaka min da kansa, zaman silifas d'ina Na gyara a k'afata, sannan Na taka ga wasu hotuna, hotona na nuna masa dana muftahu, yad'an murmusa yana ta6e baki, kafin ya ajiye cofin hannunsa ya hard'e hannayensa a k'irji, “Ba manufar wannan hoton ke d'inba, dan haka manta da wannan kawai, sai nan gaba watak'il zaki iya sanin wani abu”. Zanyi magana ya girgizamin kansa, alamar karnace komai. Idona na janye daga garesa kawai, na maida kan hoton Muftahu tareda nunashi da yatsa. Takowa yay har inda nake, ya kama hoton yana kallo tamkar yau ya fara saninsa, “Muftahu d'an uwa nane, kuma abokina, sai dai bakomai ne nake sakin jiki da Shiba, domin lokacin muna yara mutumne shi mai yawan k'arya, hakanne yasaka ko yaushe muke fad'a, babu abinda na tsana ga hallayar d'an Adam irin k'arya dacin amana, wannan halayyar tasa saita gaza barin zuciyata har girmanmu, kullum kallonsa nake bai canjaba, wannan yasakani fin yarda da harun fiye dashi, saikuma yake gwadamin wasu halaye na rashin gaskiya a lokuta da dama, ban k'ara tsinkewa da lamarinsa ba sai a time d'in da abinnan yafaru tsakanina da ke a birnin gayu, Muftahu shine Wanda yakawomin shawarar mizai hana na aureki ko ta wannan hanyar zansan wani Abu, da farko na d'ana masa tarkone, na yarda da auranki na shekara d'aya, yanda yacigaba da rawar jiki sai lamarinsa yacigaba da tsoratani, randa ya saka mana pill's a fresh milk daga ranar na yarda 100% shi maicin dunduniya tane, kuma akwai wani 6oyayyan al'amarin da yake son cimma buri, wannan yasakani kauda idanu a kansa, nabashi dukkan dama, dukda kullum Harun kan nusar dani illar hakan, amma na share komai tamkar bana gani, sai dai wannan zuwan danayi maganar da kika ta6amin a wani dare ya sakani cikin dogon nazari, daga time d'in kuma na saka idanuna akan Muftahu da Harun, zuwannan da nayi na k'arshe Nigeria, naga wani abin mamaki da ban al'ajabi. akwai wani d'aurin Aure da mai martaba yace mu wakilcesa ni da Hakeem (Wambai) amma sai Harun da Muftahu sukace zasumin rakiya, ba rakkiyarce ta sani Ankara a kansuba, yanayinsu ya nusar dani kowanne akwai manufarsa, ban kulaba mukaje muka halacci d'aurin auren, anatashi Hakeem yace shi zai wuce, Dan yanada wajen zuwa, banbi ta kansaba Dan bana d'aukar raini, karramawar da aka shirya yima mai martaba sai ta juye kaina, aka karramamu sosai, ni bammaci abincinba, sai Harun da Muftahu ne sukaci, suna tsaka da cin abincin sai aka kira Harun, bai d'aga wayar a gabanmu ba ya tashi ya fice, ko alama ban kawo komai a rainaba, muka cigaba da hira ni da Muftahu, abinda na lura da shi rabin hankalin Muftahu akan Harun yake, dan yanayinshi ya nuna, zuwa can sai shima ya mik'e ya fice, yacemin yana zuwa, fitarsa babu dad'ewa d'ayar wayar Harun tayi ring, ni mutumne dabai damu da shiga abinda babu ruwansa ba, amma a ranar saina tsinci kaina da duba wayar, bansan Number d'inba, amma nasan fuskar wadda take jikin hoton da Number ta bayyana, ba kowa bace face d'aya daga cikin matan Abie na”. “Matan Abie kuma?”. “kwarai kuwa, wannan shine abinda na gani, Wanda ya zaunamin a rai, koda Harun ya dawo yaga wayarsa kusa dani sainaga kamar baiji dad'iba, na bashi ina fad'in hajia ta kiraka, kinga kuwa yanda yanemi zubewa? humm saida Muftahu ya taimaka masa, dana tambayesa se cewa yayi wai tunkan mu taho dama kansa na ciwo, nasan ba haka baneba amma na sharesa. tunda muka taho na lura ana kallon kallo tsakanina Muftahu da Harun, kuma duk sanda hakan tafaru, Muftahu kanyi wani murmushi mai tattare da ma'anoni masu yawa, Wanda har yanzu nakasa fasarasu”. Huci na fidda daga bakina, na koma Inda na taso na kuma zama, shima saiya tako zuwa inda nake, ya durk'usa a gabana tare da d'ora hannayensa bisa Gwiwoyina, idanu na d'ago a hankali na sakasu cikin nashi, k'ok'arin janyewa na farayi, saboda wasu abubuwa danake hangowa cikin idanunsa. Amma saiya hanani wannan damar, yay wani sassanyan murmushi yana fad'in.............🤫✍🏼 Barkanmu da dawowa sister's😄🤝🏻🥰🥰🥰. *_ALLAH k'a gafartama iyayenmu😭🙏🏻_* *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣6⃣ .................“Kin shirya taimakon Mijinkine Munaya?”. A salon da yay maganar saida tsigar jikina ta tashi, nad'an lumshe idanu sannan na bud'e a kansa, muryata na rawa nace, “ni bansan komaiba. kuma ina ganin a wajen Abie yakamata ka k'ara samun haske ai, tunda yanzu yana magana”. Murmushin takaici yayi, sannan ya kamo hannuna cikin nashi, “Kinsan miyasa nabaki dukkan wannan labarin daba kowanne mahaluki ya sansu baki d'aya ba?”. Kaina na girgiza masa a sanyaye. Ya murmusa, tareda d'ora hannunsa saman cikina, hannun nasa na kalla, shima idonsa na a wajen, yace, “saboda kece wadda zata zama uwar d'ana ko 'yata, ina fatan koda nabar duniya ban cimma burina ba kibama duk abinda kika haifa labarinnan domin ya ida cimma manufata, wannan wasiyyace ga abinda zaki haifamin, dan inaji a jikina komi zaki haifamin insha ALLAH ba zai zama ragoba, sannan kuma tabbas kin cancanta, domin kece mutum ta farko dana ta6a yarda bazataci amanata ba bayan Mahaifiyata da kakannina da yayata da k'anina. daga k'arshe ina rok'onki girman ALLAH ki sanarmin da abinda kika Sani game dani, dan tabbas nasan kinsan wani Abu, nasha auna fik'irarki a ma'auni kuma ina samunta dai-dai, dan haka batun 6oyemin ma kibarsa zuwa yanzu, kinga Abba jibine zasu koma, to lallai rayukansu tana cikin had'ari kuma komai zai iya faruwa, saboda a yanzu mak'iyansa sunyi shirin dayafi na farko ma, a zatonsu Abbanki yasanar dani komai ne. ni kuma ban ta6a wannan maganar dashiba, sannan Abie da kike magana likitoci sunyi gargad'in kar'a tuna masa da abinda ya wuce yanzun, saboda gudun dawo da hannun agogo baya, kuma kodama na tambayesa zai iya dakatar dani yace ya yafe, ni kuma nariga nataso da BURIN 'DAUKAR FANSA, a cikin zuciyata da kwanjina, Ni nasan Yaya nayi jiyana, yau d'ina ma a wahale take kasantuwa, dan haka nakeson gyara gobena da goben 'ya'yana da dukkan ahalina, inason sanin dalilinsu nama mahaifina hakan, inba hakaba bazan ta6a samun kwanciyar hankaliba”. Nad'an muskuta domin gyara zamana, ina fad'in “shikenan, amma kabani lokacin please”. “Nabaki”. yafad'a yana mik'ewa tsaye. Binsa kawai nayi da kallo, saiya kuma bani tausayi, dukda kasantuwar rayuwarsa cikin Rud'ani, hakan bai habashi zama kamilin mutum mai tarin Nutsuwa ba, gashi da sauk'in kai, saidai idan baka fahimceshi baneba, kamar yanda na kasa fahimtarsa a farko, saika masa kallon mai girman kai. A gaba d'aya yinin wannan ranar cikin nazarin maganganun galadima na yisu, tabbas abotar Alhaji Mamman kurfe da Senator Halluru da Abbana abin dubawace, na shiga tunano wasu abubuwa danaita karo dasu a d'akin Abbana ni da Munubiya, a wani time d'in da Innarmu ta sakamu masa wani gyaran d'aki, Wanda shine sanadin shigowarmu wannan cakwakiyar kuma, na dafe kaina saboda saramin d'in da yakeyi, motsin da d'an cikina yayine ya sakani dafe cikin ina lumshe idanu, gaba d'aya kaina yana Neman kullewa, har a washe garin ranar haka naita fama da tunani, danma yana hanani, amma danaga ya matsa zan d'ora daga inda na tsaya, yanzu ma dazai fita aiki saida yamin gargad'i, yace na sauka k'asa wajensu innarmu nayi hira, to kawai nace masa, amma yana fita ban fasaba, ganin lokaci na k'ara k'urewa saina d'auki waya na shiga rubuta massage mai tsawo dazan turama Munubiya. Duk abinda takeyi a idon Galadima ne, tun d'azun yana lura da dukkan motsita ta camera d'in daya ajiye a d'akin wadda koda wasa Munaya batasan da zamanta ba, ya murmusa tareda godema ALLAH, dan yasamu damar kamata a hannu, ta wannan hanyarce kawai zaiyi amfani da ita wajen samun abinda yake buk'ata ga Abbanta, dan Abba yak'i bashi kowacce k'ofa dazai san wani abinda ya sakashi shiga wannan halin, alhalin yaga tarin damuwoyi a idanunsa, masu kuma matuk'ar muhimmanci a aikinsa. Wayarsa tai 'Yar k'ara alamar Munaya na sarrafa wayarta, saurin saita abinda ya saka mata a wayarta bata saniba yayi, harta gama typing ta tura sak'on akan idonsa, shiga yayi ya duba, saiyaga Munubiya ta turama sak'on, yay hanzarin bud'ewa. (Galadima ya had'a wani tarko a wayar Munaya batareda ta saniba, dukkan wani Abu dazai shiga wayarta ko fita saiya gansa a wayarsa, ta wannan hanyarne yaga na yanzu, saimu bishi muga abinda Munayar ta rubuta to). _“ ‘Yar uwata, tabbas Allurafa na shirin to no galma, anzo ga6ar da lallai yakamata mu sanarma Galadima komai akan abinda muka Sani, danna fahimci lallai zatonmu yazama gaskiya, wannan sunedai ahalinnan da mukaga bayanai a Kansu, dukda nakula Abbanmu nasan basarwa, saidai bansan manufarsa tayin hakanba, bayan wannan itace damarsa ta k'arshe dazai yadda kwallon mangwaro ya huta da k'uda, sweetheart minene shawararki? dan burina dana haife cikinnan auren contract ya k'are a tsakaninmu, domin babu alak'a kuma kenan, kinga nima na samu 'yancin kaina, nayin auren din din din kamar kowacce mace”._ Babu shiri Galadima ya mik'e tsaye, jikinsa har wani tsuma yakeyi, lallai anzo ga6ar Ashe, hasashensa yazama gaskiya kenan kokuma zai zama, tomi wad'annan yaran suka sani? kenan Munaya Nada dalilinta na yarda da auren su na Contract? Mi Muftahu ya Sani gameda Munaya dahar ya d'anata a gareshi a matsayin tarko?, bayan shi yana nan yana ik'irarin yima Muftahu tarko da auren Munayar. Lallai kan yakula itama Munaya da 'Yar uwarta da Muftahu suna Neman zame masa RAINA KAMA. Baifi mintuna 15 ba da tura sak'on da Munaya tayi, saiga Munubiya ta kirata, duk Galadima yana kallo daga camera d'insa da kuma saitin wayarsa, dukda kuwa yana office ne, Munaya bata d'aga kiranba, saida ya katse sannan ita ta kirata, munubiya na d'agawa Munaya race, “Sweetheart kinga sak'ona kuwa?”. “Na gansa sweetheart, amma fa ni duk kin rikitani, kinga wata alamace data tabbatar miki ahalin Galadima ne?”. “Munu, tabbas alamomi da yawa sun nunamin hakan, sannanfa shima yasan Alhaji Mamman k'afur fa, kuma kinga ai a takardarnan munga sunan Alhaji Mamman k'fur d'in, gashi abokin Abbanmu sosai, nifa yau wlhy abubuwa masu yawa ya fad'amin game da sirrinsa, dukda kasancewarsa mutum mara yarda, duk dai da inaji a raina kamar ya fad'amin wani yankin sirrinsane danya bigi cikina be, amma ni wlhy tausayi guy d'innan yake bani da gaske”. Munubiya tayi murmushi daga can, cikin tsokana tace, “to ALLAH yabar k'auna dai, sweetheart”. “ban ganeba, k'aunar mi zai bari?”. “keda Galadima mana, ai soyayya kan fara da tausayine”. “Mtsoow dan ALLAH muyi magana mai amfani Munu, yanzu ya kika gani, danya rok'eni ALLAH akan nafad'a masa mina Sani, nikuma ina tsoron koba akansa d'in baneba Abbanmu yake cikin damuwar, karmuzo kuma muyi aikin Baban giwa”. Ajiyar zuciya Munubiya ta sauke, ta gyara kwanciyarta tana fad'in Munaya kodai mu sanar da innarmu ne kozata bamu shawara?”. “kai amma bakida hankali yasin, sokike innarmu taci k'aniyarmu Ashe, zatace miyasa tun a farkon lamarin bamu sanar mataba, k'ilama tayi fushi, Dan nima wlhy ayanzu ina ganin munyi wauta fa”. “to komadai miye munrigada mun aikata. Yanzu mafita zamu nema, mizai hana ki rok'eshi inhar bashi bane kokin fad'a Dan girman ALLAH karya tada zancen kawai, yakuma rik'e mana sirrinmu, idan kuma zai taimakemune akan Wanda kema Abbanmu barazana da mutuwa ai kingani munsamu madafa muma, kinga dai yanda sukaso cin galaba wajen kashesa, wlhy Munaya jinake kamar kar Abbanmu su dawo k'asarnan”. “Ni kaina tsoron dawowar tasa nakeji, musamman da jiya Yakuma maimaitamin, shiyyasa kawai na Yanke shawarar mu fad'a masa, idanma ba shi bane saiya taimakemu wajen gano wanene”. “to shikenan, sai naji yanda kukayi kenan, Yaya unborn d'inmu?”. “gashi nan ya isheni da motse-motse wlhy, na k'agara ma ya fito na huta, kema Yaya namu da lafiyarki?”. Cikin tsokana Munubiya tayi dariya, “aikoya fito nanda wata shekarar Munafata wani ya Shiga sweetheart”. “wlhy na kula bakida man kai Munubiya, sai anjima”. Munaya tafad'a tana yanke wayar. Galadima daga can yay wani k'asaitaccen murmushi yana shafa Kansa da cije lips, ya koma jikin kujera ya lafe yanamai lumshe idanu. 👭 🤣Galadima Kodai-kodai🤫 ************ Muna gama waya da Munubiya na sakko k'asa, babu kowa gidan dagani sai su innarmu sai jakadiya, a falon k'asa na iskesu suna hira. Jakadiya tace, “ranki ya dad'e kin fito?”. Murmushi namata, ina fad'in “na fito jakadiya, ya k'ok'ari?”. Tai 'yar dariya tana cewa “kuke fama da k'ok'ari ai, ALLAH dai ya raba lafiya”. Bance komaiba na zauna ina gaida Innarmu ta amsa tana tambayata ya jikin. “da sauk'i” na fad'a kaina a k'asa, nace, “innarmu Abba fa? ko barci yakeyi?”. “A'a sun fita ai shida Sauban tunda safe, zasuga likitansa daga nan sud'an zaga gari”. “Oh ALLAH ya dawo dasu lafiya to, zaisha yawo kam indai fita da Yaa Sauban ne”. Dariya jakadiya tayi, tace, “ai mai sunan manya sai a hankaki, shibama ya gajiya”. Inna tace, “a baya gajiya kam, ni ai birgeni yakeyi, babu ruwansa, sai tsokana da barkwanci”. “Ai tamkar gadone abin nasu, dan mai martaba lokacin yanada lafiya, dukda kasancewarsa shugaba hakan baya hanashi barkwanci da mutane lokaci-lokaci, to hakama magajin gari yake, daga bayane shi sai nasa halayyar suka canja, yazama shiru-shiru, amma shi mai sunan manya saibai canjaba kuma”. Ina jinsu nidai bance komaiba, sai murmushi danake tayasu dashi kawai. Mun dad'e a falon har su Abba suka dawo, masaukinsu ya wuce, Sauban kuma ya zauna muka cigaba da hira, tashi innarmu tayi tabi bayan Abba. Sauban ya mik'e yana cewa zaije ya watsa ruwa, itama sai jakadiya tashiga domin nunawa kuku abinda zai dafa, ganin haka natashi na nufi masaukin su innarmu. Nakama handle d'in k'ofar zan murd'a tareda yunk'urin sallana sainaji muryar innarmu kamar tana kuka, “Haba Abbansu dan ALLAH ka sanarmin damuwarka, Yaya kana cikin matsala amma ka gaza fad'ama kowa?, tunda tafiyarnan tamu ta gabato ina lura dakai baka ko barcin kirki, sannan inajinka kana sambatu cikin mafarki jiya da asuba akan kozasu kasheka bazaka bayarba, shin wai minene? kuma su waye?, nidai tun bayan haihuwar su Munubiya na fuskanci kana cikin wata damuwa, amma kullum cikin k'ok'arin 6oyewa kake, bansan minene kake 6oyewarba, haba Auwal, a tunanina yanzu munzama irin d'ayan da bazaka 6oyemin matsalaba kowacce irice, a nawa tunanin munkai bigiren raba farinciki ko sa6aninsa, ko kasan ranar da muka fita da dasu Samha naga lokacin da wani bak'in mutum yazo kuka ke6e gefe, kana kuma magana tsakaninka dashi cikin fushi”...... A rikice naji Abba ya katseta da fad'in Ai'sha kenan ido kike sakamin ban saniba?, dan kawai kin ganni da mutum saiki fassara da wani Abu, Toni banma sanshiba, dan kawai ya ganni bak'in fatane shine yake tambayata, amma daga hakan babu komai, tunba yanzuba kikemin tambayar mike faruwa ina baki amsa babu komai, miyasa bazaki yarda babu komai d'inba, ni nama matso da tafiyar tamu baya, dan doctor yakuma tabbatarmin da babu wata sauran matsala, ki sanarma Munaya ta sanar da mijinta gobe zamu koma kawai”. “gobe kuma Abbansu?”.. A fusace yace “eh!”. Ni kaina saida na razana da tsawarsa naja baya daga jikin k'ofar, da sauri nabar wajen jin alamun za'a bud'e k'ofar, tabbas akwai abinda Abbanmu ke 6oyewa da gaske, to wanene bak'in fatar da innarmu tagani tare da Abba ranar? a ranar tare dasu muka fita, saidai sun rigamu tafiya, saboda ni da Galadima mun biya asibiti wajen awo, saida akamin sannan mukabi bayansu, kenan kafin muje abin ya faru? dan tabbas na tarar Abba baya cikin walwalarsa, harna tanbayesa ko jikinsa ne? Amma yacemin a'a kansane kawai ked'an ciwo. Bansan na iso bedroom d'inmu ba saboda zirfi danayi a tunani, ko hawan benen ma bansan nayoba, juyowa nayi da sauri saboda jin an kama hannuna. ganin Galadima saina rajaza zanyi baya, da sauri ya rik'oni da k'yau yana fad'in “Nutsu mana”. Da k'yar na tattaro nitsuwa ta, shikuma ya zaunar dani gefensa, hawayrne suka shiga ziraromin a kumatu, Abbana yana cikin matsala, amma wani dalili ya hanashi fad'a, takai har inda yake jiyya ana bibiyar rayuwarsa kenan?. Ido Galadima shidai ya zubamin, bai hanani kukanba baikuma tambayeni dalilin yinsa ba, kusan 5minutes sannan ya kwanto da kaina jikinsa, jina a k'irjinsa saina fashe da sabon kuka, nanma k'ala bai ceminba, yadai cigaba da bubbuga bayana alamar lallashi, saida nayi mai isata nayi shiru sannan ya d'agomin kaina, dukkan kumatuna ya rik'e cikin tafin hannunsa, Kafin yay k'ok'arin saka idanunsa cikin nawa, cikin k'asaitacciyar muryarnan tasa mai kama da anmasa dole yace, “Haba yalla6iya, sokike ki haifamin abin cikin kwan mai saurin kuka irinkine wai shin?”. Bansan Sanda murmushi ya su6ucema fuskata ba, na lumshe idanuna saboda bana da jimirin jure kallon da yakemin, shima murmusawa yayi, sannan yakai fuskarsa dab da tawa yana huramin iskar bakinsa a saman ido. Ban iya hanashiba kusan mintuna 2 sannan ya daina, bud'e idona nayi nad'an kallesa, ya d'agamin gira yana fad'in, “ya dai?”. Cikin tunzuro baki nace, “babu komai”. “To miye abin jin haushi daga tambaya”. ‘yay maganar yana sakin kumatuna’. Binsa nayi da kallo, ganin zai fara k'ok'arin cire kaya, na mik'e zan fice, dan yanzu na lura lamarinsa kullum k'ara girmama yakeyi, baya shakkar cire kaya a gabana ko sakawa, sai dai ni na fita na bashi waje. Hannuna ya rik'o, na waro ido waje cikin mamaki. “ina zaki?”. ya fad'a cikin tsare gida. “ba wanka zakayi ba?, idan kagama zan dawo ai”. “toni dodone?”. “A'a na fad'a ina ta6e baki”. “to koma ki zauna ki kalli sadakinki”. Idanu na waro masa waje da hangame baki. Yiyai kamar bai ganniba ya basar. bai sakeniba yakuma cigaba da cire kayansa da hannu d'aya. Ni daifa k'in kallonsa nayi, dan wlhy kunya nakeji sosai, dukda 'yar shak'uwa ta shiga tsakaninmu hakan bai sa mun saki jiki da junaba, garama shi idan rashin kunyarsa ta motsa yakanyi abinda ya gadama yana basarwa a dole kar'a kawo masa raini. Yakan bani dariya sometimes, amma nima saina Basar saboda Jan aji. Iska kawai naji a cikin kunnena, da sauri na waigoshi, ganin sa dagashi sai boxer sai na juya fuskata. Bayana ya koma ya zagayo da hanayensa duka akan cikina, yayinda kansa ke a kafad'ata, muryarsa can k'asan mak'oshi yace, “miya sakaki kuka?”. Salon da yay maganar ya sakani lumshe idanu saboda tsigar jikina data tashi. Nace “kabari ka gama zan fad'a maka”. “miyasa ba yanzu ba?”. “ka saka riga to”. Murmushi yayi yana shafa cikina, “my friend sarkin tsiwa sarkin kuma Kunya, akwaiki da abubuwan bi........” Saikuma yay shiru yak'i k'arasawa, hannuna na saka na rik'e hannunsa da ke yawo saman cikina, nace, “ka k'arasa mana, akwaini da mi?”. “Humm” kawai ya fad'a yana sakina, yaja bathrobe d'insa dake jikin hangar ya sanya, saida naga ya fara k'ok'arin d'aure igiyar sannan na d'ago na kalleshi. “To mikuma kike kallo?”. Ya fad'a cikin tsare gida. Baki na ta6e ina fad'in, “miye abin kallon to?”. Ya d'an fiddo ido sannan ya matsoni, “zona nuna miki”. Nasan ko guduwa nayi saiya kamoni dan haka na duk'e ina fad'in “wash ALLAH cikina”. Tsayawa yay cak, saikuma ya tako da hanzari yana tambayar lafiya?. cikin marairaice face nace “Motsi yakeyi ALLAH”. rankwashina yayi aka yana cewa “ke d'inan ko”. Dafe wajen nayi, bai kulani ba ya shige bathroom, na harari bayansa ina masa gwalo, nasan inda banyi hakaba bakina ne zaisha wahala. Ina zaune ya fito, na d'auke kaina tamkar ban ganshiba, shima hakan yayi, ya wuce wajen frigate ya d'akko ruwa da Kofi, kujerar dake wajen karatunsa ya jawo ya zauna yana fuskantata, batareda yayi yunk'urin cire bathrobe d'in jikinsa ba, yanzun kam babu wasa a fuskarsa, ban damuba dan nasan halin kayana yanzu, yanzu zakiga yasaki jiki yana magana kamar ba shiba, anjima kad'an saiya koma Asalin Galadimansa dana fara gani a Hospital, Mara dariya mara later r😏. K'afarsa d'aya ya d'ora kan d'aya yana shan ruwa, yasha kusan rabi sannan ya cire, batareda ya ajiye kofinba ya maido dukkan hankalinsa kaina, “A kwana biyunnan kokin lura Abba yana cikin damuwa?”. d'ago idanuna nai na kallesa, a sanyaye nace, “abinda naji innarmu na masa Complain kenan yanzu, amma saiya nuna fusata”. “shine kika shigo kina kuka?”. Na jinjina masa kai batareda nace komaiba. Shima bai sake cewa komanba ya kauda idonsa daga kaina yana kur6ar ruwansa. kusan 2minutes sannan yakuma kallona, “Munaayaa mukawo k'arshen 6oye-6oye mana”. Kallonsa nima nayi, nace, “kamar ya?”. “humm” yafad'a yana cije lips, mik'ewa yayi tsaye ya ajiye cup d'in hannunsa a gabana, sannan ya shiga zagaye d'akin hannunsa goye a baya, nikam dai binsa kawai nakeyi da kallo kamar na samu television, maganarsa ta katsemin tunanina. “Munaaya! Mikuka ta6a gani a d'akin Abba ke da 'Yar uwarki?”. Zumbur na mik'e dan mamaki, “yalla6ai a ina kasan wannan?”. batareda ya kalleni ba yace “Munaya Sameer ya wuce dukkan tunaninki, dan haka fad'amin?”. Ajiyar zuciya na sauke, wadda ta tilasta masa juyowa ya kalleni, nace, “yalla6ai ba fad'a maka bane matsalar, kuskuren muhallin fad'arne da kuma makomata”. “bakida dukkan Matsala da wad'annan, idan bai danganceni ba zan d'auki matakin taimakon sirikina, makoma kuwa inada yak'inin kare martabar matata uwar d'ana ta kowanne hali”. Furicinsa yaban mamaki, dan haka nace, “matar Contract ko?”. “Well Duk yanda kika fassara dai-daine, abinda na Sani kawai wannan maganar batada nasaba da waccan, dan haka kibar kowanne a muhallinsa sai lokacin yinsa yayi”. “humm” kawai na fad'a na koma na zauna inda na tashi. Idonsa a kaina ko k'yaftawa bayayi. Na nisa sannan nafara fad'in, _“Na tabbata tunkan ka k'ulla alak'a dani saida kasan koni wacece, dan babban mutum irinka bazaiyi Abu babu wani tanadiba, banida matsala wajen maimaita maka sunana ko tarihin ahalin dana fito, kamar yanda kasani mu 'yan biyune hakan yasaka ba'a banbancemu ni da 'yar uwata, sai dai hallaya takan banbantamu ga Wanda ya sanmu, Munubiya mutumce mai hak'uri da yawan kawaici, a wajen gadon hali tabbas ta biyo mahaifiyarmu ne, sa6anin ni Munaya mai zafi da yawan tsokana, a lamarina babu ragi ko d'aga k'afa, inhar kaga nayi dogon zama da mutum babu sa6ani to ka tabbata ya tanaji matakan iya zama danine, basai amfad'a ba nima kaina nasan halayena na kamanceceniya dana Mahaifina da kuma kakata innaro, a wata litinin d'in da bazan ta6a mantawa ba sai mahaifinmu yayi wani bak'o, matsalar da aka samu shine yazo bai iske Abba a gidaba, a wannan ranar innarmuce da aiki, dan haka hak'in tarbar wannan bak'o saiya rataya a wuyanta, maimakon tayi da kanta saita saka cikinmu ni da Munubiya wani yayi”._.......................✍🏼 Mu had'u a page na gaba🤫 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu🙏🏻😭_* *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉1⃣7⃣ _..................“Da haushi na d'auki ruwan da innarmu ta bani na fita, saboda muna tsaka da kallon wani film daneke masifar sone, Munubiya dan kartaje kaiwa saita hau barcin k'arya. Tunda na shigo shegen mutumin nan ya tsura min idanu yana lasar baki, kai kace tsohon mayene yaga nama, a zafafe na dire tiren agabansa ko k'ararsa zatasa ya dawo hayyacinsa, amma wawannan yayi nisa, na buga tsaki a zuciyata zan fice, caraf ya kamo hannuna, ban dubi girmansa ba na dage na watsa masa mari, hakan kuma yayi dai-dai da shigowar Abbanmu falon. Amma d'an iskan ganin Abbanmu da marin danai masa baisashi sakin hannunaba, saida Abba ya daka masa tsawa da fad'in “SD! wane irin iskancine wannan? a cikin gidana ka kama hannun 'yata?!”. Abba na rufe baki ina kuma bashi mari na biyu, tunda naga alamar shi bunsurune. a wannan karon ya saki hannun nawa, saboda janyeni da Abba yazo yayi, Abba ya nunamin k'ofar fita, koda na fita saina la6e a corridor d'in shiga falon bak'in._ _A zafafe Abbanmu naji yana fad'in “SD ubanwa yabaka damar shigomin gida ne?”. sautin tafin bak'on na jiyo dan haka nai saurin lek'awa ta kafar labule, gani nai yana zagaye Abba yana dariya da tafi, cikin shak'iyanci yake cewa “Alhaji Auwal, Alhaji Auwal! dama kanada k'yawawan 'yammata haka? Woow nice babie, idan na samu wannan ai ko rana bazata sake ganina ba, wlhy nasan zan kwashi rom........., mari Abba ya zuba masa a kumatu, yana nunashi da yatsa, a matuk'ar fusace yace, “wlhy idan ka kuma furtawa saina datse kazamin harshenka a falonnan, wawa kawai”. SD ya shafa kumatunsa sannan ya sumbaci hannun yana hurama Abba, “Kafa birgeni Alhaji Auwal, kai jarumi, 'yarkama jaruma, kai inason irin haka mutumina uhhhhhhm mutccch”. ya k'are maganar da kuma kissing hannunsa. Banza Abba yamasa ya d'auke kai daga kallonsa yana fad'in “miya kawoka gidana?”._ _Alhaji Auwal kenan, kaima kasan dakaga SD kasan zancen, a wannan karon da albishir d'in k'arin farashi akan tayin baya nazo maka, sannan kuma damace a gareka ta k'arshe hakan, mun yanke shawarar baka naira milyan 500”. Abba yaja tsaki yana hararsa, “ka koma ka sanar ma iyayen gidan naka ina kan bakana, sannan Ku farka daga barcin da kukeyi, dan bazan ta6a badawa ba, kamar yanda ban ba da jiya ba, bazan bayar yauba, sannan gobe ma bazaku samuba, wannan kuma yazama first and last dazaka shigomin gida, inba haka ba ina mai tabbatar maka zaka aikata kuskuren da bayan bayanka ma saisunyi takaicin jin yanda zaka k'are”. “kwantar da hankalinka sarkin jarumai, tabbas zan tafi, bakuma zan sake dawowa ba balle nayi nadama Oga, ammafa bazan 6oye makaba, kana bani mamaki, kak'i bama Wanda akace ka bamawa, sannan kak'i saida mana mu masu buk'ata, shikuma wannan Abu ba tuwoba balle muyi tunanin zakacine, waikai mike damun kankane haka? ka zauna kanata rik'ema Wanda yarigada ya mutum amana, shikuma Wanda kakema tanadin bashida maraba da gawa, koda yake ashefa ga Galadiman Ku nan, koshi kakema tanadi?”. “wannan ba matsalarka bace”. Abba yafad'a cikin karsashi. “kumafa gaskiyarka wannan ba matsalata baceba, amma tabbas inada yak'inin kai zata zama taka matsalar maybe ma harda santaleliyar budurwar 'yarka, lallai labarin k'yak'yk'yawa da ahalinta zai Shiga duniya kwanannan, nabarka lafiya, ka huta”._ Da sauri nabar wajen gudun karya fito ya ganni, nakoma cikin gida ina juya wad'annan zantuka na abbamu da bak'onsa, masu tsananin wahalar fassara, mi bak'on yake nema a wajen Abba dahar yake ik'irarin sun basa zunzurutun kud'i naira na gugar naira, d'ai-d'ai har miliyan d'ari biyar? Amma dukda yawansu Abba bai firgitaba balle mik'a wuya?, sannan wanene Galadima kuma? Miyake nufi da labarina zai shiga duniya? Na shiga uku ALLAH karka bama bawannan damar cutar da rayuwata ko ahalina gaba d'aya. Munubiya data lura da halin danake cikin ta sakani gaba da tambayar, tun ina k'ok'arin 6oye mata Dan kar hankalinta itama ya tashi, harna fito fili na sanar da ita gaskiyar abinda naji da kuma gani, harma Wanda na aikata. Hankalin Munubiya ya tashi sosai itama, nanfa muka Shiga kullawa da kwancewa Munason gani gaskiyar lamarin, amma mun kasa kama bak'in zaren, fita kuwa mun koma yintane a d'arare saboda tsoron furucin mutuminnan. a wata ranar talata da Abba zai dawo daga tafiya sai innarmu ta sakamu gyaran d'akinsa saboda kanta namata ciwo. muna tsaka da aikin sai muka tsinci wani file da yasha k'yak'yk'yawar adana a awani akwati dake cikin wardrobe d'in Abba, to dama da biyu muke aikin, harda bincike akan Neman hasken maganganun da mukaji ranar, jikinmu har rawa yake muka bud'e wannan file, a shafin farko mukaci karo da wani Abun daya kuma rikita tunaninmu”. 👇🏻 *_Tabbataciyar wasiyya ga ahalina, koda ace na kwanta dama kafin cimma burina ko mik'a wannan sak'on amana ga Wanda ya cancanta, to na shaida muku da cika umarnina na ida nufina a garesu 'ya'yana ko 'yan uwana, inason Ku isar da wannan amana da aka bani ga ahalin wannan masarauta............”._* “iya nan rubutun ya tsaya, muka bud'e shafin na biyu kozamuga sunan masaurar da Abba ke magana da k'arashen zancensa, amma sai sunayen mutane muka gani a k'alla sunkai goma. Wucewa mukayi shafi na uku, a dai-dai wannan lokacin Abbanmu ya shigo d'akin batare da mun Ankara ba, wata hargitsatstsiyar tsawa mai tsinka hanji ciki da zukata ya daka mana yana fad'in “ku harkunkai girman da zakumin bincike a d'aki a matsayina na mahaifinku? mi kuka sani akan wannan takardar dahar kuke binciken abinda ke cikinta? Yaushe kuka koma la6e?”. haka Abba ya rikice gaba d'aya muma ya rikita mu, ya dinga zabga masifar dahar tajawo hankalin jama'ar gidanmu, indai tak'aice maka bayani har innarmu saida fushin Abba ya shafa ranar, hakanne yasani fahimtar Abba ya gane naji komai a ranar. munshiga damuwa a time d'in matuk'a, dukda hak'urin da muka bashi yak'i saurarenmu, ya d'au tsawon lokaci yana fushi damu kafin ya daina. bayan komai ya daidaitane kuma wani yammaci mun fito daga school saiga motocika a jere suna tsula uban gudu a titi, wucewarsu tamkar iska yasakani fad'ar bak'ar magana ga manyan k'asarnan har 'yan uwana na tayani. Sai kuma mukaji sunanka a bakin wani saurayi da 'yammata biyu. Wannan ganinaka ne yasakani dawoma Munubiya da abinda ya wuce, saboda sunan Galadima da mukaji saurayinnan ya ambata, sai muka dinga tunanin kokaine Wanda muka ta6aji a furucin bak'on Abba?. ga kuma sunan masarauta da muka gani a rubutunsa, dukda bamuji sunan ainahin masarautarba kuma, balle mu tabbatar da kaid'inne.. Ganinmu dakai na biyu kuma saika bani haushi, dan ganinka mutum mai yawan izza, sainaga bebekin Abba daya saka kansa had'ari akan Wanda shi baima damu da damuwar kowaba sai tasa gakuma tarin girman kai Dana hango tartare dakai”. (Kafayi hak'uri, gaskiyata nake fad'a, guntun murmushi kawai Galadima yamata baice uffanba) taci gaba da fad'in “Wannan ne dalilin yimaka tsak'i a asibiti, idan har baka mantaba, har dogarinka d'aya yataho da zummar d'aukar mataki amma ka dakatar dashi da fad'in ya barni”. Galadima ya murmusa alamar bai mantaba. Nace, “ka tuna kenan?”. “Na tuna kwarai da gaske, dan bancika manta abuba saidai idan na d'aukeshi mara muhimmanci, amma a time d'in ai banga face nakiba, shiyyasa banida tabbacin kece, saidai na muku kallo d'aya a lab da muka iskeku keda sisters d'inki, ni nama zata Ku 'yan uku ne ai”. “Umyim, amma a time d'in babuma Wanda zai d'auka Kasan da zamanmu a lab d'in, dan gaisuwar da ake maka ma, kamak'i amsawa sai d'aga hannu, hakanne ya tunzurani na fito daga lab d'in, dasu munu sukace kainema kabada jinin da za'a sakama feena ban yardaba”. Baki Galadima ya d'an ta6e yana shafa kwantaccen sajensa, ya d'agamin gira d'aya yana fad'in “bazaki fahimta bane yalla6iya. yanzu labarin da kika bani ya farune duk a wace shekara?”. Na d'an ya mutsa fuska ina fad'in bamai nisa bace, dan ko 2years cikakku baza'a k'ulla ba, Muna Exam d'in NECO nema, dan har results d'inmu suka fito aka fara biyan JAM Abbanmu ya biyama sauran 'yan uwanmu amma banda ni da Munubiya, sai baba k'aramine ya biya namu, so munfara karatu dai babu dad'ewa muka shirya da Abbanmu saboda magana da dad d'insu Ayusher yamasa Yakuma sake bashi hak'uri. tundaga nan komai yazama Normal. Amma kaikanka yakamata kayi mamakin yanda a kwanaki kad'an na amince da tayin auren Contract d'in da kukaimin, dukda ba waccan binciken namu kawaine keda alak'a da amintar tawaba, akwai wani dalili daya shafi ahalina”. Mik'ewa Galadima yayi yana salute d'ina, yace, “kin cancanci yabo my friend, dukda tabbas a farkon aurenmu kema kina cikin zargina akan turoki akai gareni tun farko, amma yanda kike halayyarki da d'abi'unki sai kika kauda hankalina, a tunani na dukkan mutum dazai kwantarmin dakai yaringa nuna tsorona to tabbas wannan mutumin sunamsa *MAGE MAI KWANCIYAR 'DAUKAR RAI* a wajena, amma kece mutum ta farko kuma mace data iya mayarmin murtanin magana kai tsaye, batare da shakka ba, sai dai inason Sanin minene alak'arku da Muftahu to?”. “muftahu kuma? babu wata alak'a bayan wadda kasani, dan tare Na fara ganinku ai”. Takowa yay zuwa inda yake zaune a da, ya koma saman kujerar ya zauna, “kin tabbatar babu alak'a ta kowane fanni?”. “miyasa kake kokwanto? inhar zaka kasa gaskatani a nan bai kamata ka aminta da zancena Na farkoba kenan?”. Ya murmusa yana fad'in “kozaki gaji Abba ne?”. Nace, “akan me?”. “jaridanci mana, naga kin shahara wajen iya bincike”. Mik'ewa nayi saboda k'afata tafara yaamm alamar jinina yana buk'atar motsawa, nafara d'an takawa. hannaye kawai ya hard'e a k'irji yana bina da kallo, saida nad'an zagaya d'akin kafin nabashi amsa da fad'in “yalla6ai kasan wani Abu kuwa?”. Kansa ya girgizamin kawai. Nace, “humm nifa nan daka gani, kwakwalwata tana aiki fiyeda yanda kake aiki da agogo”. “really?”. “baka buk'atar jayayya”. Ya d'aga kafad'a yana ta6e baki, “hakane kuma”. Sharesa nayi na zauna a bakin gadon danna d'an mik'e, a haka najawo filo na kwanta k'afafuna a k'asa. Tasowa yayi ya dawo ya zauna saman k'aramin table d'in gaban sofa, jinai kawai ya kama k'afata ya d'ora saman cinyarsa yana matsamin a hankali. Da mamaki na d'ago kai na kallesa. Ido d'aya ya kannemin yana d'an ta6e gefen bakinsa, ya maida kallonsa ga k'afar. Sabon salo, na fad'a a raina. a fili kuma nace, “yalla6ai kaine......” Bai bari na k'arasa ba yay saurin fad'in, “ba dole na taimaki lafiyar abin cikin kwan ba”. Harara na dalla masa ina janye k'afata, ya kalleni da mamaki, “ya haka? ko haushi kikajine?”. “miye zai Sani jin haushin? saika bari idan yafito duniya ka matsa tashi k'afar”. “oh ni Sameer naga ta kaina”. “zama kaga ta k'afa bata kaiba, Sunan nakama bazaka iya fad'arshi da r ba”. “oh nan kuma kika dawo?”. Matsawa nayi baya saman gadon sosai batareda na bashi amsaba. shima saiya taso ya hawo gadon, hakan yasani yunk'urawa zan sauka na bar masa, fan nasan hawan nasa bazai haifar da d'a mai ido ba, yasa hannu ya rik'eni, “yalla6iya ai saikin maimaita mikika fad'a dalla-dalla”. “lah wasafa nake maka, kaga rigar wankace a jikinka kaje ka cire kar mura ta kama ka”. “Ai kinga dai-dai kenan”. Yay maganar yana k'ok'arin kwance igiyar rigar. Hannunsa nayi azamar rik'ewa ina marairaice face alamar yaji tausayina. Baki ya ta6e yana ture hannuna, na kuma k'ank'ame nasa nak'i bari. Murmusawa yayi, ya kwanto gefena tareda sakani jikinsa ya rungume. “Nace please wankama zanyifa, zafi nakeji”. Maidani yayi ya kwantar, cikin kunnena yace, “kedai fad'i gaskiya, ko kina son a.......”. Rufe bakinsa nayi da tafin hannuna ina kukan shagwa6a, ya shiga k'ok'arin cirewa amma nak'i bari, shi dariyama na bashi, irin wannan hak'ilo haka. duk yanda yaso na barsa k'i nayi, saida barci yafara fisgata hannun ya zame. Kansa ya girgiza kawai yana murmushi, a fili ya furta “mai bakin tsiwa”. Ya k'are maganar da sumbatar goshinta yana gyaramata kwanciya a jikinsa. Ya tsira mata idanu yana kallon yanda take fidda numfashi a hankali, a zahiri idonsa a kanta, amma zuciyarsa maganganunta taketa cud'awa, shi baima ta6a ganin mace yarinya k'arama mara tsoro da shiga rikita-rikita irinta ba, bata gudunma shiga had'ari? ya sauke ajiyar zuciya yana tashi zaune, k'afafunta yashiga mammatsa mata a hankali, aikam harda gyara kwanciya su madam munaya, yad'an murmusa, yasan ko'a d'azun tanaso fa, amma iyayi yasata hanashi ya mata. Ya d'auki tsawon lokaci yana mammatsa mata jikinma gaba d'aya, yayinda zuciyarsa kuma ke tattance bayananta dalla-dalla, daga k'arshe sauka yay daga gadon ya fice zuwa d'akin sirrinsa, duk abinda tafad'a yasamu sabon file ya bud'e masa, baya wasa da evidence komai k'ank'artarsa, balle ma nata ya wuce Na wasa, ya dad'e yana rubuce-rubucensa kafin ya koma kan Computers, sunan SD kawai ta ambata masa, dan haka yafara searching gameda SD d'in kawai, babu abinda ya fahimta akan hakan, dama baiyi tunanin fahimtarba, waya ya d'auka ya kira Nuren, bayan sun gaisa yace, “Nureddin acikin yaransu Tanderu kasan SD?”. “SD! SD! kai anya kuwa? amma dai ina zuwa bani mintuna 30”. “ok saina jika”. Galadima Na yanke wayar ya nemo number d'in Abba da bakowa ya sani d'innanba yafara aiki a kansa, dukkan Contact d'in ciki suka bayyana, d'aya bayan d'aya ya dinga binsu yana nazarin adadin kiran da aka ta6ayi, sau nawa aka kira Abba sau nawa ya kira shima? Mafi yawa ma kiransu yafi yawa, yad'an murmusa yana wasa da tsinken hannunsa a kan la66a da nazarin yanda zai 6ullo musu, dan duk hanyar daya kamata yayi bincike an d'auki mataki a kanta, tsawon lokaci bai fahimci komaiba, sai zuwacan wata dabara tafad'o masa, nutsuwa yay yana sarrafa Computer's d'in cikin tsantsar kwarewa da gwaninta, ya kafa musu tarko ne a wayar innarsu Munaya, dan ya tabbata watan watarana zasu iya kira ko sak'o, amma abinma haushin saiya iske wayar inna a kashe, ya dafe kansa, saifa da yacema dady aringa barin wayar a kunne. Babu shiri ya d'auki waya ya kira daddy, bayan sun gaisa yaymasa maganar kunna wayar innar. cikin mamaki Dady yace, “ai a kunne take koda yaushe, Change ma baya k'arewa nake kuma sakata, idankuma zan zo nan nakan sanarma Jafar shima ya kula, amma ina zuwa dai”. Galadima ya amsa da to, amma k'asan zuciyarsa tana mamaki. babu dad'ewa Abba ya sake kiransa, “Ashe Change ne ya k'are babu dad'ewarnan ban lura ba, amma gashinan Na sakata”. “to Dady, Na gode sosai”. Sunayin sallama da Dady Kiran Nuren Na shigowa, d'agawa yayi, Nuren yace, “inagafa brother hanya d'ayace dazata saka musan shi wanene SD d'in, dan abinda Na lura dashi baya amfani da hakan ta kowanne fanin yanar gizo, maybe da full name yake amfani. yanzu zan sayi ticket insha ALLAH zanje domin bincika a wajen Malam Saminu, nasan ya magantu yanzu, zai amsa mana dukkan tambayarmu”. “ok hakan yayi, idan ka fahimci bai saniba karka takurashi, ka binciki yarinyarnan itama, koma ka fara bincikarta dan ita bama wayo ta cikaba sosai, k'ila kafi samu cikin sauk'i a wajenta, abinda yasa Malam saminu baison fad'ar komai, babbar 'yarsa cikin 'ya'yan Alhaji balala wani ya mata ciki, kuma sun dai-daita akan idan ta haihu za'ama yaran aure, wannanne yasakashi tsoron fad'ar komai, dan karya lalata waccan alak'ar, dan tabbas yasan yana fad'a auren bazai yuwuba, to nima banason shiga hak'in kowanne ahali akan aikina, shiyyasa nabashi dama kaga bankuma waiwayarsa ba, yanzu haka yarinyar ta haihu kwana hud'u kenan, amma shi yaron ya kawota nan Dubai ta haihu ne, a nufinsu bayan haihuwar da sati d'aya zasu dawo Nigeria a d'aura musu aure sannan su dawo Dubai d'in, dan Alhaji balala baya son abinda zai 6ata record d'insa, kuma mamar yaronce ta Dage sai anyi auren dan ita mutuniyar kirkice, dan haka mu bama Malam Saminu wannan damar”. Ajiyar zuciya Nuren ya sauke, cikin mamaki yace, “duk ya akayi kasan wannan brother? ”. galadima ya murmusa, yana fadin “Nuren kenan, to bara nayi copy d'in my mata, kwakwalwata tana aiki fiyeda yanda kake aiki da agogo, nasha fad'a maka bada kwanji kawai ake yak'i ba, sai anhad'a da dabarun tunani dana nazari, so kad'an nafad'a maka daga abinda ya shafi Malam Saminu, kaidai saina jika kawai, a time d'in da zakuyi maganar ka tabbatar ka had'a Communication dani ok?”. “babu damuwa aljanin munaya”. Dariya sosai Galadima ya shiga tuntsurawa da iskancin Nuren, wato shima ya maida Aljani yau, wlhy yaronnan yagama rainashi, wai Aljanin Munaya, d'an iska zan kamaka ai. Kashe komai yayi ya fito daga d'akin, bai koma cikiba saiya sakko k'asa, ya iske Sauban kad'ai a falo, shima shigowarsa kenan daga asibiti yake. Galadima ya zauna yana fad'in “jirgi sarkin tashi daga ina?”. Dariya sauban yayi, yace, “kai Yaya, nine kuma jirgin?”. “Kamafi jirgi ai. Wane shiri kakeyi gameda zuwa bautar k'asarka Nigeria”. Sauban ya 6ata fuska kamar zai fasa ihu “yaya yanzu fa ca za'ayi saina koma 9ja har zaman 1year?”. Hararsa Galadima yayi, “to zakayi anan k'asar ne?”. “Ni Yaya ALLAH da anayi da nayi, a manta da bautar k'asar kawai mana, nayi joining masters d'ina”. K'aramin tsaki Galadima yayi, yay crossing k'afarsa yanama Sauban wani kallon bammasan amsar dazan bakaba, saida ya d'auki wasu mintuna sannan yace, “rashin yin ai bazai zama matsalar kowaba sai taka, bakuma zaka gane hakanba sai nan gaba idan ALLAH ya kaika inda bakayi zatoba, idan kace bazakayiba it's better, nidai ai nayi nawa ko. tashi kabani waje”. Ganin ransa ya 6aci Sauban ya marairaice fuska zaiyi magana, amma sai Galadima ya d'aga masa hannu, sannan yamasa nuni da k'ofa alamar ya fice masa. Fita Sauban yayi yabarsa, shifa tsakani da ALLAH zaman masarautar ne baya son yi shi kad'ai. Galadima ya girgiza kai kawai yana fad'in “ALLAH ya shiryeka, gata kasamu tunda katashi kaga komai basai ka nema ba”. Jakadiya data fito ta rissina tana fad'in “Ashe ka shigo magajin gari, barka da dawowa”. Murmushi Galadima yayi, yanason matarnan saboda halaccin datake wa rayuwarsu, “yauwa jakadiya, ya gidan?”. “lafiya lau Ranka ya dad'e, a shirya abinci ko?”. Agogon dake tsintsiyar hannunsa ya kalla, sai kuma ya maida ga jakadiya, “bar abincinan jakadiya, akwai Inda zanje”. “to ALLAH ya dawo dakai lafiya”. Hannu ya d'aga mata kawai sannan ya tashi ya fice. mashin ya hau yafita. Abba dake can gefe a harabar gidan tsakanin wasu flowers yana hutawa ya sauke ajiyar zuciya, tundaga fitowar Galadima har hawansa mashin da fitarsa akan idonsane, rufe idanunsa yayi yacigaba da tunaninsa da tun d'azun yake zaune a wajen yanayi. Asibiti Galadima ya nufa, yay kici6us da Aunty Mimi Na shirin tahowa gida ta huta, ta kalleshi da mamaki, “my k'ani dawowa kayi?”. Gefen girarsa yad'an shafa da d'an yatsa d'aya, “eh , ina zakije k?”. “gida zanje nad'anyi wasu abubuwa”. “ok sai kin dawo”. yafad'a yana ida shigewa, ita kuma ta fice. Momma Na zaune tana waya da papi, ya zauna d'aya a kujerun yana kallonta cikeda sha'awa, uba da 'Yar sun birgeshi, juyawa yay ya kalli gadon Abie, barci yakeyi, har Momma ta gama wayar ison Galadima Na kan Abiensa ko k'yaftawa bayayi, shi kad'ai yasan mi zuciyarsa take sak'awa. “Muh'd daga ina haka?”. Maganar Momma ta katse masa tunani. Janye idonsa yayi daga kan abie ya maido ga Momma, “Daga gida Momma, har yanzu barcin Abie yakeyi?”. “eh tunda ka Fita bai farkaba, mike faruwa naganka cikin damuwa?”. Huci ya furzo daga bakinsa, zaiyi magana sai kuma yayi shiru. “Nifa tsiyata dakai kenan Muh'd, Yaya Abu nacin ran mutum bazai iya fad'ama kowa a taimakeshi da shawara ko addu'a ba, kaga yanda jijiyar kanka ta tashi kuwa? Haba Muh'd Sameer d'ina, kaifa yanzu ubane, girmanka ya k'aru, aringa rage damuwarnan da miskilanci mana, ni ALLAH ma yasa ba haka kakema d'iyar tawaba?”. “kai Momma”. ya fad'a amarairaice cikin 'Yar shagwa6a. Murmushi tayi tace “to fad'amin mike faruwa?”. Yay d'an tsaki, “Ni ai Momma bammasan ta ina zan fara baneba”. “kafara ta sama kawai”. Momma ta fad'a tana dariya. Shima dariyar yayi kad'an sannan ya gyara zama, kuma maida muryarsa k'asa-k'asa yayi yana maganar ahankali, tsaf ya zayyanema Momma yanda sukayi da Munaya, ya d'ora da fad'in “Amma kinsan wani Abu kuwa Momma?”. “a'a saina fad'a dear”. “uhm gani nake kamar bakomai ta fad'a minba, ta 6oye wasu abubuwan dai kamar, saidai bansan dalilinta ba. Momma ta jinjina kai tana murmushi, “To Muh'd mizai hana kacigaba da binta a hankali, nasan zata fad'ama sauranma, ni aganina kamar tana ganin kaima ka kasa yarda da itane shiyyasa tafad'i wasu tak'i fad'in wani, idan har ka yaba da hankalin matarka yakamata ka fara sakin jiki da ita wajen Neman shawararta da sakata cikin wasu al'amura naka Na tabbata itama zata fara fad'a maka nata”. “gaskiya kika fad'a Momma, dan naga fa'idar hakan kwarai da gaske, zan kula insha ALLAH. ya addu'oin Abie akwai saura?”. “saura kad'an, gashi bakuyi wasuba”. “mai k'arfin yince tazama sai a hankali, daga barci sai barci take yini”. “ALLAH Sarki d'iyata, ai tanama k'ok'ari, dama idan ciki ya fara tsufa hakane, ALLAH dai ya sauketa lafiya”. “To amin Momma”. Sun cigaba da 'yan hirarrakinsu har zuwa lokacin da Abie ya farka..................✍🏻 *_inata gaisheku da yawa da yawa, comments naku Na sakani nishad'i over🥰🥰🥰🥰🥰😍😍😍😘😘😘_*. I love you wijiga-wijiga sister's🥰🥰🥰🥰 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🤚🏻✋🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣8⃣➖1⃣9⃣ .................Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gadon Na nufi Na watsa ruwa. Ina tsaka da shafa mai Samha ta shigo, saida tayi sallama nabata izinin shigowa sannan, ledar hannunta Na kalla ina fad'in “mikika samo mana 'Yar Uncle?”. Cikin dariya ta zauna kan sofa tana cewa “kayan dad'i ne Aunty gimbiyarmu, alfarma nazo nema wajenki keda Uncle”. Hankalina gaba d'aya Na maido kanta, “Alfarmar mi kuma?”. “Aunty gimbiya please ki lalla6a Uncle ya barki muje birthday d'in k'awata Dhibya, ALLAH yarinyarnan tana sonki sosai, kullum hirarki”. Nad'an zaro ido “kai Samha yaza ai naje wani birthday da wannan cikin? kuma kema kinsan bazai bariba tunda Na 'yammatane”. “kai aunty, cikin saikace Wanda yayi wani k'ato, kumafa a cikin gida za'ayi wlhy, iyamu goma ne kawai”. “to naji, ALLAH yasa ya bari, mikika kawo mana a ledar?”. “yes my sweet aunty, wannan wani sari ne yamin k'yau a wani shagon da muke zuwa siyan kaya, shine nayi alk'awarin siya miki, Uncle Sauban ya cikamin na siya, yanzu Na kar6o please ki gwada muga”. Dariya nayi, nace, “inye kaga 'Yar Uncle Anfara jink'an iyaye, to amma ni ina na iya saka sari?”. “kowama koya yayi nidai ki saka muga dan ALLAH”. “to shike nan bara na gwada, ALLAH ya saka da alkairi, ina alfahari da d'iyata”. Samha ta fita tana dariya, nikuma na warware kayan, masha ALLAH sarin ya had'u gaskiya, farine anmasa kwalliya da pink and silver kad'an-kad'an. Na saka rigar, sai dariya ta kamani, saikace wata bafulatana🤭🤣. Warware zanin nayi, tofa anan akeyinta, dan ban iya nad'awaba, na tsaya gaban mirror inata gwadawa amma na kasa, dariya ta kamani, yau naga takaina, Samha ta had'ani da aiki. Tunda ta fara k'ok'arin d'aura zanin sarin yana tsaye a k'ofa, ya hard'e hannayensa ak'irji kawai yana kallonta, kamar zaiyi dariya saboda yanda taketa murd'e-murd'en d'aurawa. A hankali ya taka zuwa inda take, jinai kawai andafa min kafad'u ta baya, na d'ago a tsorace muka had'a ido ta cikin mirror, fuskarsa babu walwala, ya d'agamin gira d'aya, maida idona k'asa nayi, yayinda shikuma ya juyo dani ina fuskantarsa. Gwiwarsa d'aya ya saka a k'asa ya dogare d'aya, nidai kallonsa nake mizaiyi?. Batareda ya kalleni ko min magana ba ya zare zanin dake tattare a hannuna, nikam kamar wata sokuwa saina sakar masa. Yiyay kamar zai warware zanin, nayi saurin rik'ewa, ya d'ago fararen idanunsa yanamin alamar na saki, ban iya musa masaba na sakar masa. Shima sai bai yaye dukaba ya dai-daitashi, ammakina sainaga yana nad'amin, babbar magana Galadima da nad'a sari. Dazai saka wanda a ke sokewa a gefen kugu sai yayi dawani salon daya sakani zabira saboda sak'onsa yajemin har kwalwar kai, ya d'ago ya kalleni yana wani miskilin murmushi da d'agamin gira. Sai kawai na lumshe ido dan naji kunya wlhy. Ya mik'e tsaye yana daidaitamin na kafad'ar shima, nidai harya gama ban bud'e idoba. baiyi magana ba ya warware reborn d'in kaina, da sauri na bud'e idon, yanda yawani tsareni da idanu sai nakasa jurewa na maida na rufe. Cumb ya d'auka yahau gyaran kai, to nikma naga abinda yafi k'arfina yau d'innan, wai dama guy d'innan ya iya abin mata ne?. Bai barni ba saida ya gama yanda yakeso dani, ya zubamin ido kawai batareda yace komai ba. nikuma nakasa bud'e idona na kallesa, ahankali yafara busamin iskar bakinsa saman idona, dole nafara marmar da idanu, dainawa yayi, na bud'e idon ahankali a kansa, kuma matsoni yayi muka Zuba juna ido ko k'yaftawa bamayi, gashin dake neman shigarmin ido ya saka d'an yatsa ya matsar, na maida idanun na lumshe ina sauke k'aramar ajiyar zuciya. Shima nannauyan numfashi ya sauke kafin yaja da baya, wardrobe d'insa ya nufa, jin yabar wajen saina bud'e idona, duk jikina ya saki, kallo d'aya namasa na d'auke kaina na juya ga mirror Dan naga yanda ya maidani, murmushi nayi ina saka hannu na gyara gashina, nima na yarda da gaske nayi kyau. Nakuma d'ago ido da nufin sake kallon kaina sainaganshi a bayana, sark'a ya ziro a ya sakamin tareda gyara zamanta ta zauna sosai a k'irjina, ya janye gashina ta baya yana sak'ala sark'ar, nidai nawa idone, ya gama ya cire d'an kunen dake kunnena ya sakamin na sark'ar, sannan ya mannani da jikinsa yana zagayo hannunsa duk biyu saman matashin cikina, hannuna ya kama yana sakamin bangles, cikin k'asaitacciyar muryarnan tasa yake magana cikin kunnena, “haka dama sari kema Afirikawa k'yau?”. Murmushi nayi, na d'ago idona muna kallon juna ta cikin mirror, haryanzu hannayena na cikin nasa yana saka bangles d'in da guda d'ai-d'ai. Ya lumshe idanu yana shanshanar wuyana, jikina yafara rawa, babu shiri na saka hannuna d'aya daya gama saka bangles d'in na shafo gefen kumatunsa, cikin rawar murya nace “please kabari yalla6ai”. Batareda ya dainaba cikin sark'ewar harshe yace “mizaisa na daina? yalla6iya”. Yanda yake min akan dokin wiya da yanda hannunsa d'aya ke canja salo a jikina sainayi k'ok'arin juyowa garesa, ko hakan zaisa yabari d'in. Ashe dama ma na sake bashi, gaba d'aya yawani rikice kamar ba Galadiman Dana saniba. Hannunsa ya sak'alo kuguna yana kuma matsoni jikinsa sosai, yasaka d'ayan hannun ya tallafo kaina tareda d'ora la66ansa akan nawa. Kasa jurewa nayi, na mik'a masa wuya kawai, harda bada gunmawa nima........ Tofa munga idi, daga gyaran sari🙆🏽😹. Samha tataho da karsashinta dantaga ko Munaya ta saka, daga nan ta nuna mata yanda zata nad'a zanin sarin, tunda tasan bata iyaba, ko kad'an babu Wanda yaga shigowar Galadima, Dan babu kowa a falon, jakadiya ta tafi asibiti itada Sauban da innarsu munaya, aunty Mimi kuma barci takeyi, Dady kam yanacan baya inda ya maida lambun tunaninsa, itako Samha tana bama Munaya sari takoma d'aki danta bata lokaci ta shirya a tsanake. Sallama d'aya kawai tayi ta turo k'ofar tana kwala kiran “Aunty gimbiyarmu kin saka?”. Galadima dayake Neman fara zirmawa yay hanzarin sakin Munaya, da sauri naja baya nima, dan kamar a sama mukaji muryar Samha. Itama Samha baya ta koma da sauri gabanta na fad'uwa, Dan ganin Wanda batayi zatoba a d'akin. ALLAH ma yaso bataga komaiba, lokacin datake sako k'afarta a d'akin Galadima ya janye bakinsa yana k'ok'arin matsawane baya. Wata uwar harara mai kad'a hanji da hanta ya zubama Samha, hakanne yasakata yin baya da sauri ta koma. Nikam kasama d'aga ido nayi balle na kalleshi dagashi har Samhar, saima wani yaam nakejin jikina tamkar zan fad'i. Lura da hakan da yayine yasakashi azamar rik'o hannuna, na shige jikinsa ina sauke tagwayen ajiyar zuciya, dagani harshi idanu kowa ya lumshe, tsawon lokaci muna a haka munkasa sakin juna, ahankali na shiga k'ok'arin janye jikina, bai hananiba yabani damar barin jikinsa, ra6awa nayi ta gefensa na wuce, na koma saman sofa na zauna ina dafe kai, juyowa yayi yana kallona, kafin yatako shima zuwa bakin gado ya kwanta, k'afafunsa na k'asa duka, yayinda yay filo da hannayensa yana lumshe idanu. Duk munyi shiru d'akin tamkar babu wata halitta mai numfashi a cikinsa, kowannenmu shiyasan mi yake sak'ama zuciyarsa. K'arar wayarsace ta sakamu d'an firgita mu duka, duk sai muka zubama wayar ido tamkar wani ojuju. harta tsinke bai d'aukaba, saida aka sake kira sannan ya cirota daga aljihun wandonsa yay picking. Muryarsa vary low yace, “Nuren Yaya dai?”. Mamaki da al'ajabi ya cika Nuren, yakuma Ciro wayar daga kunnensa ya duba Dan tabbatar da Galadima ne kuwa?, lallai shine, maida wayar yayi a kunne yana fad'in “brother lafiyarka kuwa?”. Taune lips nashi yayi, ya yanke wayar, dan indai ahaka zasuyi wayarnan bazai fahimci komaiba, ajiye wayar yayi yatashi ya shige bathroom. Da kallo k'asa-k'asa kawai na iya binsa, amma nakasa ko kwakwkwaran numfashi. Daga can kuwa Nuren kwashewa yayi da dariya saboda tuno wani Abu, (to su Nuren dai dama bariki sune manyanta🤣), dariya yakeyi iya iyawa yana dukan kansa, daya fara tsagaitawa saiya kuma saka wata, saida yayi ta ishesa sannan ya daina, ya rik'e ha6a yana fad'in “oh ni su brother ansan takan tsiya, ina ganinsa lab-lab Ashe d'anba sauk'ine, toma uwar miye na d'agamin wayar tunda yasan yafara sauka a network🤣, yakuma saka dariya saikace wani sabon kamu.😬 Galadima kam ruwa ya sakarma kansa kawai, ya dafe bango da hannu biyu ruwan na kwarara saman kansa, sai faman taune lips yakeyi shi kad'ai, yayi da zuciyarsa ke sak'awa da kwancewa, saida ya ji k'arfi-k'arfi sannan ya kashe shower d'in yaja bathrobe d'in ya saka yana faman sauke 6oyayyar ajiyar zuciya. Inda yabarta anan ya fito ya isketa, kallo d'aya yamata ya d'aukekai, bakin gadon ya zauna yana goge kansa da k'aramin towel, yajawo wayar da d'ayan hannun ya danna kiran Nuren. Bugu d'aya Nuren d'in ya d'aga, da k'yar yasamu ya danne dariyarsa, “brother wai miya farune naji muryarka haka? nifa ka tadamin hankali”. “Ba komai, shin kajene?”. Nuren ya toshe bakinsa gudun kar dariya ta kufce masa, Sameer d'an rainin wayone ALLAH, wai babu komai, to naji babu komai aje a haka. “wai kana jina kuwa?”. Galadima yafad'a. “Oh sorry brother network nayin wasa, gani a gidan, amma bankai ga shiga inda takebane”. “ok tom kaje, amma kabar wayar a kunne, inason naji komai”. Nuren yace “to”. Da sallama ya shiga d'akin, sai wani ciccin magani yake. Farhat dake zaune bakin gadon d'akin ta zabga tagumi ta d'ago kai tana kallonsa, yayin da wasu hawaye ke shirin zubo mata. Kujera guda d'aya dake d'akin ya jawo ya zauna. Farhat ta share hawayen kumatunta, murya a sanyaye tace, “yayana dan ALLAH kayi hak'uri, wlhy ina missing d'in families d'ina da karatuna, dan ALLAH idan kasheni zakayi ka kasheni kawai na hutama rayuwa ma ni gaba d'aya”. Murmushi Nuren yayi, idonsa a kanta yace, “bazan kashekiba Farhat, dan bakimin komaiba, kamar yanda na sanarmiki mahaifinkine yaja miki, ki kwantar da hankalinki, insha ALLAH zaki koma gidanku kwana kusa, yanzuma dukba wannanba, wata tambaya nazo yimiki, ALLAH yasa zaki bani had'in kai?”. Kanta ta jinjina masa tana kuma share sauran hawayen, “insha ALLAH inhar nasani zan fad'a maka”. “good girl ”. ‘cewar Nuren yana gyara zama’. “Farhat nasan kinsan duk yaran Abbanki ko?, ina nufin masu masa hidima a office ko a gida?”. “Eh nasan mafi yawansu, dan ina zuwa wajensa a Office, kuma wasu acikinsu sukanzo gidanma”. “Masha ALLAH, kokin san SD?”. “SD!?”. “eh shi”. “gaskiya a yaran Abbana dana sani babu wani mai suna SD”. “okay, amma ko wani mai Something sunan dazai iya kasancewa full name bazaki iya hasasowa ba?”. Shiru tayi ta lula duniyar nazari, shidai Nuren ya zauna mata idanu yana kuma jinjina ma ubangiji akan yin k'yak'yk'yawar hallita, dan Farhat black beauty ce masha ALLAH. A jiyar zuciya ta sauke, “yaya inaga kamar dai akwai wani Sagir dauda dana Sani, amma bansan aikin da yake a k'ark'ashin Abbanmu ba, sai kuma ya Shareffudden k'anin Aunty Umma, sai Steven Daniel”. “shi Steven d'in wanene shi a gidanku, itama Aunty Umman haka?”. “Driver d'insu Mom ne, shike kaisu anguwa, ita kuma Aunty Umma matar Abbanmu ce ai, itace amaryarsa”. “Uhyim”. Nuren yafad'a yana jinjina kai. “Dan ALLAH yayana in tambayeka mana?”. “ina saurarenki”. “laifin mi Abbana yamuku hakane?”. murmushi Nuren yayi, “karki damu nangaba kad'an komai zai wuce, kuma bashi yay laifinba, wanine yayi na kusa dashi”. “to ALLAH yasa Ku kamashi, amma dan ALLAH karkuma Abbana komai”. “insha ALLAH babie”. Murmushi Farhat tayi, Nuren kuma ya mik'e tsaye idonsa a kanta. “babu dai wata Matsala ko?”. Cikin shagwa6ar data saba tace, “please ko TV ka samin, banajin dad'in zaman hakanan”. “Am sorry to say dear, har kibar gidannan dokace, babu television, babu phones, amma way not nakawo miki irin Hausa novels d'innan danaga mata na karantawa?”. Idonta ya cika da kwalla, “ayya yayana wlhy ban iya karatun hausaba sosai, yana bani wahala”. Ido yad'an zaro waje, yace, “saboda mi? Keba bahaushiya bacene?”. “bahausa mana”. ‘tafad'a cikin turo bani irinnan ta6ararru’. Baki ya ta6e yana kama hanyar fita, “zaki cigaba da kad'aicinki ashe kuwa”. Ganin zai fice da sauri tace, “please ka siyo zan fara koya to”. “it's better”. ‘yafad'a yana ficewarsa’. Saman gadon ta fad'a ta fashe da kuma mai ban tausayi. Duk abinda ke faruwa Galadima najin komai ta waya, Munaya ma na zauna a sofa har yanzu tana satar kallonsa, amma batajin miyake saurare da ya nutsu haka. Cire wayar yafara k'ok'arin yi ya jiyo muryar Nuren na fad'in “hello brother kana jina?”. Galadima yace, “eh”. “okay duk kaji aimi ta fad'a ko?”. “duk najiku, saika samin ido akan duk d'unsu, a bincikomin komai daya shafesu”. “indai wannanne insha ALLAH angama, amma ni a ganina banda wannan Shareffuden d'in datace, domin babu wani kamanni a cikin nashi sunan, ballema tace k'anin step mom natane”. “Humm Nuredeen kenan, shifa mak'iyi ba'a rainashi, mutane da yawa sukan d'auki cinnaka ba komaiba, amma idan yacijesu sukan ji cizon har a ransu, dan haka karka ta6a d'aukar mage mafi sauk'i akan kare, itama idan taga nama citakeyi”. “wannan gaskiyane brother, ALLAH yabamu sa'a”. “amin ya rabbi, naji kuna maganar buks da ita, kaje ka samo mata dukkan Wanda take buk'ata, har English novels d'in, sannan ak'ara tanadar mata dukkan abinci mai k'yau datake so”. “insha ALLAH angon Munaya”. Girgiza kai kawai Galadima yayi ya yanke wayar. Kallon Munaya yayi suka had'a ido, saita janye cikeda basarwa. Shima tashi yayi ya koma gaban mirror, duk uzirinsa yayi ya gama sannan yamatsa ga wardrobe ya ciro kayan dayake buk'ata. Ganin haka Munaya tazame ta kwanta cikin kujerar yandama bazata gansaba. Baki kawai ya ta6e yacigaba da saka kayansa. Bayan yagama yamatsa kusada ita, “tashi ki canja kaya ki rakani wani waje”. Fuska Munaya tad'an yatsina, kamar zatace wani Abu saikuma ta yunk'ura zata tashi kawai, hannunta ya kama ya taimaka mata ta tashi zaune. fita yayi abinsa. Hakan yasata fahimtar zai jirata a falo kenan. Bata 6ata lokaciba ta canja kayanta da atanfa skt da riga, takawo after dress ta saka sannan ta nad'a Vail d'in rigar, d'as ta fito itada cikinta, kamar ka saceta ka gudu abinka. Tunda ta fito ya zuba mata idanu, ko k'yaftawa bayayi, saida yaga tana gabda k'arasowa garesa ya basar yana mik'ewa. Gaba yayi tabisa abaya, yandama yake taka steps d'in benen dolene ya birgeka, duk takunsa nakan idonta, yayinda itama take binsa daki-daki a hankali. Babu kowa a falon, dan haka suka fice basu nemi kowanba. A mota yana tuk'i da sauraren karatu itakuma tana latsa waya suna charts a families group d'insu. Sai murmushi take zubawa, duk abinda take yana kallonta ta gefen ido. Sun isa wani k'aton shagon saida kayan babies, duk abinda kake buk'ata zaka sameshi indai na yarane daga 1year zuwa 15. Itadai mamaki ya ishi Munaya, miye nawani kawota nan? yabari a haihun mana ma. Tarba ta musamman aka musu, hakan ya tabbatar ma Munaya yasan mai shagon kenan, dan yanda aketa girmamasu sai abin ke bata mamaki. gashi indiyanci sukeyi bata fahimtar maganganunsu. Itadai tana zaune hankalinta ya rabu gida biyu, wajensu Galadima da kuma wasu mata biyu da yaransu uku dabazasu wuce 7-7years ba, yaran k'yawawa masha ALLAH, ga wayo. Galadima ya juyo zai mata magana saiya lura da inda ta zubama idanu, shima shagala yay a kallon yaran, iyayensu na za6ar kaya amma su suna tibirewa sai Wanda sukeso za'a d'auka. Munaya sai zuba murmushi takeyi, dan suntafi da imaninta, shima murmusawa yayi yana lasar lips, kafin ya d'auke kansa ya maida ga Wanda suke maganar. Zuwa can gardama ta hark'ume tsakanin yaran akan wani game da iyayen ke dubawa maybe zasu saya musu ne. Kuma games d'in suna kusada Munaya ne, d'aya a cikin yaran ya d'akko yazo wajen Munaya yana tambayarta wai “Aunty wannan yafi dad'i aidai ko?”. Munaya bata fahimceshiba, dan yayi maganane da yaren dabata ji, dan haka saitayi murmushi ta tambayesa yanajin English?. Yaron ya d'aga mata kai alamar eh. Ta kuma murmusawa, duk abinda ke faruwa a idon Galadima ne. Da turanci munaya tace, “yarona kai kata6a irin wannan game d'inne?”. Murmushi yamata shima, yace “aunty akwai dad'i ma sosai, ranar saida na cinye kharan a gidansu ma”. “da gaske?”. munaya tafad'a tana dafa kafad'arsa. Kansa ya d'aga mata, cike da d'oki yace, “Aunty na koya miki?”. Munaya ta d'aga masa kai. Game d'in ya d'ora a cinyarta, ya danna wasu Number, sai kuma ya zubasu cikin d'aya, duk suka shige. Cikin mamaki munaya tace “mikenan to?”. Shima dariyarsu ta yara yayi, yace “Aunty ai wayo na miki, Abu guda d'ayane, amma sainayi ammafani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d'aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had'a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d'aya ne na had'aka kuma akan Abu guda d'aya kacal”. Sosai abun ya birge munaya, tayi dariya har hak'oranta na bayyana, jawo yaron tayi a jikinta ta rungume. Iyayensa dake tsaye suna kallonsu tun d'azun duk sukayi dariya suma, sannan suka matsa kusada munaya suna bata hannu alamar gaisuwa. itama ta mik'a musu suka gaisa, d'aya tace sunanta Radha, d'ayar kuma tace Anjali, munaya ta fad'a musu nata suna itama, sannan takamo hannun saran yaran tana tambayarsu suma, d'aya yace vanish, d'ayan kuma Anjun, duk kumatunsu ta sumbata tana sakama rayuwarsu albarka. Wadda tace sunanta Radha tace “kiyi hak'uri da surutun Vishnu shi baya gajiyane ko kad'an”. Munaya tace babu komai. Daganan sukai gaba, munaya tana binsu da kallo tana murmushi, yaran sai waigenta suke suna d'aga mata hannu. Sunje wajen biyan kud'i akace subar kud'insu inji mai shagon, da mamaki suka tambayi wanene? Mikuma yasa ya barmusu. Mai kar6ar kud'i ya murmusawa yana fad'in mijin matarcan da kuka gaisane mai shagon ai. Munaya batasan mike faruwaba taga sun dawo, godiya suka shiga yimata, ta tambayesu akan me?. Suka bata amsa da cewar mijinta bai kar6i kud'in kayansu ba. Murmushi tayi, k'asan ranta tana mamakin dama shagon na Galadima ne?. Sun katse mata tunani da tambayar kozasu samu number ta, babu musu tabasu sukayi sallama suka tafi. Maida kallonta tayi ga Galadima dake zaune yanata latse-latsen laptop tamkar baisan mike faruwaba, da alama yana duba kayane ko wani Abu, dan time to time Wanda yake gefensa yakan nuna masa wani yanki na kayan dake shagon, shikuma ya waiga ya kalla, idan bai hango sosaiba saiya kalla ta cikin Computer d'in dake tareda cctv cameras d'in shagon. Munaya tace kai mutuminnan akwai son kud'in tsiya, kai komai kana saidawa, wata zuciya tace idan bai nemi kud'iba dame zai kula da mahaifinsa?. “hakane kuma”. ta fad'a a fili tana sauke ajiyar zuciya. Kusan mintuna 15 saitaga ya taso ya nufota. Zama yay kujerar kusa da ita yana fad'in “sorry friend na barki ke kad'ai. kin gaji mu tafi ko?”. Munaya tad'an yamutsa fuska tace “ba sosaiba”. Ya d'an murmusa, “ok tunda baki gajiba kozaki d'an mana taimako ni da abin cikin kwan?”. Hararsa tad'anyi, itafa haushin wannan abin cikin kwan dayake fad'a takeji. Hannu yasa ya dafe bakinsa yana fad'in “maida wuk'ar”. A tare suka dinga zagayawa cikin shagon, dayake babbane sosai, kayan yarane kuma zalla a wajen, komai bibbiyu take d'auka, baice komaiba, dan yasan dai bai wuce tana had'awa da cikin 'Yar uwarta Munubiya bane. Sund'an d'iba kaya babu laifi, yabada ATM d'insa aka d'auka harda na wad'ancan matan, yaran shagonne suka kai musu har cikin mota. Yanzuma haka suka taho tamkar kurame. Kowa da abinda yake sak'awa.... Danja data tsayar damune yasakashi juyowa yad'an kalleni, ganin hankalina nakan wasu yara 'yan makaranta dake mota yace, “dama haka kike da son yara?”. Juyowa nayi Na kalleshi, amma saiya d'auke kai tamkar bashine yay maganarba ma. Nima maida kaina nayi ga yaran, a kuma time d'inne muka sami damar barin wajen. Saida muka fara tafiya nabashi amsa da “yalla6ai kenan, waye zaice baison yaro, a duniya babu abinda yafi k'uruciya dad'i”. Kad'an ya juyo yad'an kalleni yana fad'in “really?”. Nima kallon nasa nayi ina fad'in “na tabbata amsarnan kowama zai baka idan ka tambayesa”. Bai kalleniba yanzun kam, hankalinsa naga tuk'insa, yace, “ALLAH ya kawoka duniya lafiya abin cikin kwan”. “shiru namasa bance uffanba”. Har muka isa gida kuma babu Wanda ya sake magana a cikinmu. Saida yay parking motar a harabar gidan sannan ya juyo gareni, ina niyyar bud'ewa Na fita ya ruk'o hannuna. kallonsa nayi da mamaki, yawani ci magani irin babu raininnan, kamar zanyi magana saikuma nayi shiru muka zubama juna ido, kowannenmu zuciyarsa Na bugawa da sauri-sauri. Cikin k'asaitarnan tasa yace, “Addu'a nayi amma jan aji yahanaki amsamin da amin”. Ni dariyama ya bani wai jan aji, hakanne yasakani murmusawa kad'an ina k'ok'arin janye idona daga cikin nasa, amma saiya hanani hakan, nace, “na amsa ai, bakaji bane kawai”. “aiba kurma kika auraba”. Uhm wannan aure ana tak'ama dashi, Na fad'a a raina, a fili kuma nace, “a zuciya Na amsa”. “k'arya haramun, banji wannan sak'onba a tawa zuciyar”. Da mamaki Na waro idanu waje ina fad'in “ban fahimceka ba”. Lips d'insa yad'an ciza da hak'ora yana matsoda fuskarsa dab da tawa, gashi ya sark'eni da idanu nakasa matsawa, d'an yatsansa ya d'ora saitin zuciyata, muryarsa k'asa-k'asa tamkar mai rad'a yace, “zuciyoyi aminan juna sukan kar6i sak'on juna alokacinda d'aya ya aikashi ga d'aya, karki jahilci kanki har yanzu akwai sauran dama”..... Yana gama fad'a ya saki hannuna, tareda bud'e motar ya fice. Galala nabisa da kallo tamkar wata sokuwa, nakasa motsi nakasa fassara zantukansa da ma'anarsu. Tsawon mintunan dahar bayin gidan sungama kwashe kayan da mukazo dasu ban fitoba, bud'ewa naji anyi, hannunsa kawai ya mik'omin alamar nakama Na fito. tamkar sokuwa haka Na d'ora hannun cikin nasa, ya kamoni ahankali Na fito, maimakon ya sakeni saiya jawoni Na shige jikinsa, ya d'ora kansa a dokin wuyana, cikin kunnena yace “wasu bayanan basa buk'atar fassara, ayanda sukazo ahaka ake barinsu, karki zurfafa tunani, dan yana kawo ciwon kai da hana Hutu”. Ya d'ago kaina tareda janye jikinsa yana d'agamin gira da salute d'ina, ya juya zuwa cikin gida. Binsa kawai nakeyi a baya tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki. A falo muka iske duka ahalin gidan, har Momma dazata kwana yau a gida, Abba ne kawai babu, muduka sun birgemu, Dan hira suke ta nishad'i da girmama juna. Dagani harshi gaishesu mukayi, Sauban da Samha dasuka k'arasa da kayanda da bayi suka shigo dasu suka sakko daga samanmu suna mana sannu da zuwa. Ni kad'ai Na amsa, Galadima hannu kawai ya d'aga musu. Momma tace, “kuje ku huta mana”. mik'ewa mukayi duk a kunyace, ina gaba a yanzu yana baya, suduka da kallon sha'awa suka bimu, dad'i da farinciki Na ratsa zukatansu, innarmu harda kwalla suka cika idonta, Wanda ita kad'ai tasan fasaarar kayanta. ★★★★★★★ Da daddare Galadima Na zaune akan sofa ya d'aura k'afafunsa saman teble yana latsa laptop, yayinda Munaya ke zaune a tsakkiyar gado tana karatun wani English novel na Galadima, buk d'in love story ne dan haka taketa faman zabga murmushi, lokaci-lokaci yakan d'ago ido ya kalleta, saboda idan tayi murmushi yakan jiyo sautinsa. Maida kansa yayi, yacigaba da aikinsa dayakeyi akan numbers d'in layin Abba na sirri, kwatsam sai maganar yaron d'azu na shago mai suna Vishnu ta fad'o masa a rai. *_Aunty ai wayo na miki, Abu guda d'aya ne, amma sainayi amfani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d'aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had'a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d'aya ne na had'aka kuma akan Abu guda d'aya kacal._* Saida yakuma maimaita maganar kusan sau uku a ransa, kafin ya kalli Munaya da dukkan hankalinta ke kan Novel, “Friend!”. Ya kirata a nutse. Da “na'am” Na amsa ina kallonsa, saikuma Na janye saboda wandon jikinsa baiko rufe masa cinyaba, sai k'aramar riga mara hannu. Yace, “mikika fahimta ga zancen abokinki na shago?”. “abokina? waye abokina?”. Tasowa yayi dagashi har laptop d'in da coffee d'insa ya hawo gadon, nima saina tashi zaune sosai. Ya zauna ta gefe tareda ajiye mug d'in hannunsa a drowa d'in gefen gadon, laptop d'in kuma a saman gadon d'ayan gefensa. hannu ya mik'amin alamar nazo. Ban musa masaba Na matso, ya kamoni ya sakani a jikinsa, dan tsakkiyar k'afafunsa ya sakani, saina zame Na kwanta na d'ora kaina a cinyarsa, (dama wajen lak'ewa nake nema🤪). Ya kar6i buk d'in hannuna ya ajiye gefe, ya d'ora hannunsa a saman cikina. Kuma maimaita masa tambayar nayi. Ya shafa sajensa yana cije lips, “miyasa wataran kike da basarwa”.. “ni d'in?”. ‘nafad'a ina nuna kaina da kallonsa’. Bai bani amsaba yace “ina nufin yaron d'azun”. “Oh sorry”. nafad'a ina gyara kwanciyat. Nace, “wai Vishnu? ”. Kansa ya d'aga min “to amma wace maganace tasa? tazama abin nazari yalla6ai?”. “game”. “game! game!” nashiga fad'a ina k'ok'arin tunanowa. “okay, wai yanda yafad'i yaci game d'in?”. “Uhhm”. ya fad'a a tak'aice.. Nikuma saina murmusa, “to dukda dai bansan ma'anar d'aukar maganar da muhimmanciba amma anawa tunanin yana nufin _abinnan mabanbantane, amma saiyayi amfani dasu cikin Abu d'aya, kuma sukai masa aiki iri d'aya, sannan duk shi kad'ai ya sarrafasu akan Abu d'aya bawai yayi tarayyar da wasu mutane da yawa bane ko aikinsa had'aka,_ wannan itace fahimta ta ga zancen nasa”. Lumshe ido Galadima yayi, ya duk'o a hankali ya mannamin Sumba mai k'au a goshi. Sannan ya d'akko novel d'in ya damk'amin a hannu, yajawo laptop d'insa yacigaba da aikinsa. Kallon mamaki kawai na zuba masa, kokad'an ban fahimci muhallin maganar tasaba da son fashin bak'i. Batareda ya kalleni ba, idonsa akan system d'insa yace, “kallonfa?”. Janye idona nayi ina ta6e baki. Shima saiya ta6e nasa alamar yaganni kenan. karatuna nacigaba shima yacigaba da aikinsa yana shan coffee time to time. Yayi aiki mai tsawo kafin yasaki wani murmushi da ajiyar zuciya, ya kalli munaya da barci ya kwashe, fuskarta ya shafa yana kuma sakin wani murmushin, “tabbas gaskiya Vishnu ya fad'a, mutum d'ayane ke amfani da Numbers daban-daban wajen kiran Abba munaya, duk wadda yagama da ita bazai sakeba, tagama aikinta, a wannan karon lallai kunyi aiki da basira, wadda harta birkita tunanin Sameer, kuna kiran Abba da mabanbanta Numbers wad'anda kunrigada kun gama shirya matakan da kowacce number bazata sake aikiba, shima kansa ya d'auka mutane daban-dabanne ke kiransa. O ALLAH wannan shine bada k'afa, to ai inkunsan wata bakusan wataba kuma, Muhammad Sameer ruwane, idan bakasha yanzuba zakasha anjima, idan kak'i kuma k'ishirwa ta kasheka. Inhar tarkon dazan d'ana zai d'annu dai-dai, tabbas zan cafke kurayen daji mai duhuwa a wannan karon”. ‘Ya k'are maganar da jan hancin munaya yana kuma sumbatar goshinta’. Kwanciya ya gyara mata sosai, ya ja bargo ya lullu6a mata sannan yaje bayi ya d'auro alwala, kamar yanda ya saba ya raya wannan dare da nafilfili da godiyar ALLAH, kafin yazo ya kwanta gefen munaya zuciyarsa na cike da annashuwa da farinciki, kaikace komai yayi done ne. Addu'a ya musu sannan yasakata jikinsa barci ya Lula dashi shima. Nima mai d'aukar rahoto bara nad'an rintsa my sweet sisters😉🤩......................✍🏻 Duk Wanda yaga ban amsa massage nashiba yamin afuwa, nayi up date WhatsApp d'inane🥰🥰🥰🤝🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu👏🏻😭_**_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣8⃣➖1⃣9⃣ .................Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gadon Na nufi Na watsa ruwa. Ina tsaka da shafa mai Samha ta shigo, saida tayi sallama nabata izinin shigowa sannan, ledar hannunta Na kalla ina fad'in “mikika samo mana 'Yar Uncle?”. Cikin dariya ta zauna kan sofa tana cewa “kayan dad'i ne Aunty gimbiyarmu, alfarma nazo nema wajenki keda Uncle”. Hankalina gaba d'aya Na maido kanta, “Alfarmar mi kuma?”. “Aunty gimbiya please ki lalla6a Uncle ya barki muje birthday d'in k'awata Dhibya, ALLAH yarinyarnan tana sonki sosai, kullum hirarki”. Nad'an zaro ido “kai Samha yaza ai naje wani birthday da wannan cikin? kuma kema kinsan bazai bariba tunda Na 'yammatane”. “kai aunty, cikin saikace Wanda yayi wani k'ato, kumafa a cikin gida za'ayi wlhy, iyamu goma ne kawai”. “to naji, ALLAH yasa ya bari, mikika kawo mana a ledar?”. “yes my sweet aunty, wannan wani sari ne yamin k'yau a wani shagon da muke zuwa siyan kaya, shine nayi alk'awarin siya miki, Uncle Sauban ya cikamin na siya, yanzu Na kar6o please ki gwada muga”. Dariya nayi, nace, “inye kaga 'Yar Uncle Anfara jink'an iyaye, to amma ni ina na iya saka sari?”. “kowama koya yayi nidai ki saka muga dan ALLAH”. “to shike nan bara na gwada, ALLAH ya saka da alkairi, ina alfahari da d'iyata”. Samha ta fita tana dariya, nikuma na warware kayan, masha ALLAH sarin ya had'u gaskiya, farine anmasa kwalliya da pink and silver kad'an-kad'an. Na saka rigar, sai dariya ta kamani, saikace wata bafulatana🤭🤣. Warware zanin nayi, tofa anan akeyinta, dan ban iya nad'awaba, na tsaya gaban mirror inata gwadawa amma na kasa, dariya ta kamani, yau naga takaina, Samha ta had'ani da aiki. Tunda ta fara k'ok'arin d'aura zanin sarin yana tsaye a k'ofa, ya hard'e hannayensa ak'irji kawai yana kallonta, kamar zaiyi dariya saboda yanda taketa murd'e-murd'en d'aurawa. A hankali ya taka zuwa inda take, jinai kawai andafa min kafad'u ta baya, na d'ago a tsorace muka had'a ido ta cikin mirror, fuskarsa babu walwala, ya d'agamin gira d'aya, maida idona k'asa nayi, yayinda shikuma ya juyo dani ina fuskantarsa. Gwiwarsa d'aya ya saka a k'asa ya dogare d'aya, nidai kallonsa nake mizaiyi?. Batareda ya kalleni ko min magana ba ya zare zanin dake tattare a hannuna, nikam kamar wata sokuwa saina sakar masa. Yiyay kamar zai warware zanin, nayi saurin rik'ewa, ya d'ago fararen idanunsa yanamin alamar na saki, ban iya musa masaba na sakar masa. Shima sai bai yaye dukaba ya dai-daitashi, ammakina sainaga yana nad'amin, babbar magana Galadima da nad'a sari. Dazai saka wanda a ke sokewa a gefen kugu sai yayi dawani salon daya sakani zabira saboda sak'onsa yajemin har kwalwar kai, ya d'ago ya kalleni yana wani miskilin murmushi da d'agamin gira. Sai kawai na lumshe ido dan naji kunya wlhy. Ya mik'e tsaye yana daidaitamin na kafad'ar shima, nidai harya gama ban bud'e idoba. baiyi magana ba ya warware reborn d'in kaina, da sauri na bud'e idon, yanda yawani tsareni da idanu sai nakasa jurewa na maida na rufe. Cumb ya d'auka yahau gyaran kai, to nikma naga abinda yafi k'arfina yau d'innan, wai dama guy d'innan ya iya abin mata ne?. Bai barni ba saida ya gama yanda yakeso dani, ya zubamin ido kawai batareda yace komai ba. nikuma nakasa bud'e idona na kallesa, ahankali yafara busamin iskar bakinsa saman idona, dole nafara marmar da idanu, dainawa yayi, na bud'e idon ahankali a kansa, kuma matsoni yayi muka Zuba juna ido ko k'yaftawa bamayi, gashin dake neman shigarmin ido ya saka d'an yatsa ya matsar, na maida idanun na lumshe ina sauke k'aramar ajiyar zuciya. Shima nannauyan numfashi ya sauke kafin yaja da baya, wardrobe d'insa ya nufa, jin yabar wajen saina bud'e idona, duk jikina ya saki, kallo d'aya namasa na d'auke kaina na juya ga mirror Dan naga yanda ya maidani, murmushi nayi ina saka hannu na gyara gashina, nima na yarda da gaske nayi kyau. Nakuma d'ago ido da nufin sake kallon kaina sainaganshi a bayana, sark'a ya ziro a ya sakamin tareda gyara zamanta ta zauna sosai a k'irjina, ya janye gashina ta baya yana sak'ala sark'ar, nidai nawa idone, ya gama ya cire d'an kunen dake kunnena ya sakamin na sark'ar, sannan ya mannani da jikinsa yana zagayo hannunsa duk biyu saman matashin cikina, hannuna ya kama yana sakamin bangles, cikin k'asaitacciyar muryarnan tasa yake magana cikin kunnena, “haka dama sari kema Afirikawa k'yau?”. Murmushi nayi, na d'ago idona muna kallon juna ta cikin mirror, haryanzu hannayena na cikin nasa yana saka bangles d'in da guda d'ai-d'ai. Ya lumshe idanu yana shanshanar wuyana, jikina yafara rawa, babu shiri na saka hannuna d'aya daya gama saka bangles d'in na shafo gefen kumatunsa, cikin rawar murya nace “please kabari yalla6ai”. Batareda ya dainaba cikin sark'ewar harshe yace “mizaisa na daina? yalla6iya”. Yanda yake min akan dokin wiya da yanda hannunsa d'aya ke canja salo a jikina sainayi k'ok'arin juyowa garesa, ko hakan zaisa yabari d'in. Ashe dama ma na sake bashi, gaba d'aya yawani rikice kamar ba Galadiman Dana saniba. Hannunsa ya sak'alo kuguna yana kuma matsoni jikinsa sosai, yasaka d'ayan hannun ya tallafo kaina tareda d'ora la66ansa akan nawa. Kasa jurewa nayi, na mik'a masa wuya kawai, harda bada gunmawa nima........ Tofa munga idi, daga gyaran sari🙆🏽😹. Samha tataho da karsashinta dantaga ko Munaya ta saka, daga nan ta nuna mata yanda zata nad'a zanin sarin, tunda tasan bata iyaba, ko kad'an babu Wanda yaga shigowar Galadima, Dan babu kowa a falon, jakadiya ta tafi asibiti itada Sauban da innarsu munaya, aunty Mimi kuma barci takeyi, Dady kam yanacan baya inda ya maida lambun tunaninsa, itako Samha tana bama Munaya sari takoma d'aki danta bata lokaci ta shirya a tsanake. Sallama d'aya kawai tayi ta turo k'ofar tana kwala kiran “Aunty gimbiyarmu kin saka?”. Galadima dayake Neman fara zirmawa yay hanzarin sakin Munaya, da sauri naja baya nima, dan kamar a sama mukaji muryar Samha. Itama Samha baya ta koma da sauri gabanta na fad'uwa, Dan ganin Wanda batayi zatoba a d'akin. ALLAH ma yaso bataga komaiba, lokacin datake sako k'afarta a d'akin Galadima ya janye bakinsa yana k'ok'arin matsawane baya. Wata uwar harara mai kad'a hanji da hanta ya zubama Samha, hakanne yasakata yin baya da sauri ta koma. Nikam kasama d'aga ido nayi balle na kalleshi dagashi har Samhar, saima wani yaam nakejin jikina tamkar zan fad'i. Lura da hakan da yayine yasakashi azamar rik'o hannuna, na shige jikinsa ina sauke tagwayen ajiyar zuciya, dagani harshi idanu kowa ya lumshe, tsawon lokaci muna a haka munkasa sakin juna, ahankali na shiga k'ok'arin janye jikina, bai hananiba yabani damar barin jikinsa, ra6awa nayi ta gefensa na wuce, na koma saman sofa na zauna ina dafe kai, juyowa yayi yana kallona, kafin yatako shima zuwa bakin gado ya kwanta, k'afafunsa na k'asa duka, yayinda yay filo da hannayensa yana lumshe idanu. Duk munyi shiru d'akin tamkar babu wata halitta mai numfashi a cikinsa, kowannenmu shiyasan mi yake sak'ama zuciyarsa. K'arar wayarsace ta sakamu d'an firgita mu duka, duk sai muka zubama wayar ido tamkar wani ojuju. harta tsinke bai d'aukaba, saida aka sake kira sannan ya cirota daga aljihun wandonsa yay picking. Muryarsa vary low yace, “Nuren Yaya dai?”. Mamaki da al'ajabi ya cika Nuren, yakuma Ciro wayar daga kunnensa ya duba Dan tabbatar da Galadima ne kuwa?, lallai shine, maida wayar yayi a kunne yana fad'in “brother lafiyarka kuwa?”. Taune lips nashi yayi, ya yanke wayar, dan indai ahaka zasuyi wayarnan bazai fahimci komaiba, ajiye wayar yayi yatashi ya shige bathroom. Da kallo k'asa-k'asa kawai na iya binsa, amma nakasa ko kwakwkwaran numfashi. Daga can kuwa Nuren kwashewa yayi da dariya saboda tuno wani Abu, (to su Nuren dai dama bariki sune manyanta🤣), dariya yakeyi iya iyawa yana dukan kansa, daya fara tsagaitawa saiya kuma saka wata, saida yayi ta ishesa sannan ya daina, ya rik'e ha6a yana fad'in “oh ni su brother ansan takan tsiya, ina ganinsa lab-lab Ashe d'anba sauk'ine, toma uwar miye na d'agamin wayar tunda yasan yafara sauka a network🤣, yakuma saka dariya saikace wani sabon kamu.😬 Galadima kam ruwa ya sakarma kansa kawai, ya dafe bango da hannu biyu ruwan na kwarara saman kansa, sai faman taune lips yakeyi shi kad'ai, yayi da zuciyarsa ke sak'awa da kwancewa, saida ya ji k'arfi-k'arfi sannan ya kashe shower d'in yaja bathrobe d'in ya saka yana faman sauke 6oyayyar ajiyar zuciya. Inda yabarta anan ya fito ya isketa, kallo d'aya yamata ya d'aukekai, bakin gadon ya zauna yana goge kansa da k'aramin towel, yajawo wayar da d'ayan hannun ya danna kiran Nuren. Bugu d'aya Nuren d'in ya d'aga, da k'yar yasamu ya danne dariyarsa, “brother wai miya farune naji muryarka haka? nifa ka tadamin hankali”. “Ba komai, shin kajene?”. Nuren ya toshe bakinsa gudun kar dariya ta kufce masa, Sameer d'an rainin wayone ALLAH, wai babu komai, to naji babu komai aje a haka. “wai kana jina kuwa?”. Galadima yafad'a. “Oh sorry brother network nayin wasa, gani a gidan, amma bankai ga shiga inda takebane”. “ok tom kaje, amma kabar wayar a kunne, inason naji komai”. Nuren yace “to”. Da sallama ya shiga d'akin, sai wani ciccin magani yake. Farhat dake zaune bakin gadon d'akin ta zabga tagumi ta d'ago kai tana kallonsa, yayin da wasu hawaye ke shirin zubo mata. Kujera guda d'aya dake d'akin ya jawo ya zauna. Farhat ta share hawayen kumatunta, murya a sanyaye tace, “yayana dan ALLAH kayi hak'uri, wlhy ina missing d'in families d'ina da karatuna, dan ALLAH idan kasheni zakayi ka kasheni kawai na hutama rayuwa ma ni gaba d'aya”. Murmushi Nuren yayi, idonsa a kanta yace, “bazan kashekiba Farhat, dan bakimin komaiba, kamar yanda na sanarmiki mahaifinkine yaja miki, ki kwantar da hankalinki, insha ALLAH zaki koma gidanku kwana kusa, yanzuma dukba wannanba, wata tambaya nazo yimiki, ALLAH yasa zaki bani had'in kai?”. Kanta ta jinjina masa tana kuma share sauran hawayen, “insha ALLAH inhar nasani zan fad'a maka”. “good girl ”. ‘cewar Nuren yana gyara zama’. “Farhat nasan kinsan duk yaran Abbanki ko?, ina nufin masu masa hidima a office ko a gida?”. “Eh nasan mafi yawansu, dan ina zuwa wajensa a Office, kuma wasu acikinsu sukanzo gidanma”. “Masha ALLAH, kokin san SD?”. “SD!?”. “eh shi”. “gaskiya a yaran Abbana dana sani babu wani mai suna SD”. “okay, amma ko wani mai Something sunan dazai iya kasancewa full name bazaki iya hasasowa ba?”. Shiru tayi ta lula duniyar nazari, shidai Nuren ya zauna mata idanu yana kuma jinjina ma ubangiji akan yin k'yak'yk'yawar hallita, dan Farhat black beauty ce masha ALLAH. A jiyar zuciya ta sauke, “yaya inaga kamar dai akwai wani Sagir dauda dana Sani, amma bansan aikin da yake a k'ark'ashin Abbanmu ba, sai kuma ya Shareffudden k'anin Aunty Umma, sai Steven Daniel”. “shi Steven d'in wanene shi a gidanku, itama Aunty Umman haka?”. “Driver d'insu Mom ne, shike kaisu anguwa, ita kuma Aunty Umma matar Abbanmu ce ai, itace amaryarsa”. “Uhyim”. Nuren yafad'a yana jinjina kai. “Dan ALLAH yayana in tambayeka mana?”. “ina saurarenki”. “laifin mi Abbana yamuku hakane?”. murmushi Nuren yayi, “karki damu nangaba kad'an komai zai wuce, kuma bashi yay laifinba, wanine yayi na kusa dashi”. “to ALLAH yasa Ku kamashi, amma dan ALLAH karkuma Abbana komai”. “insha ALLAH babie”. Murmushi Farhat tayi, Nuren kuma ya mik'e tsaye idonsa a kanta. “babu dai wata Matsala ko?”. Cikin shagwa6ar data saba tace, “please ko TV ka samin, banajin dad'in zaman hakanan”. “Am sorry to say dear, har kibar gidannan dokace, babu television, babu phones, amma way not nakawo miki irin Hausa novels d'innan danaga mata na karantawa?”. Idonta ya cika da kwalla, “ayya yayana wlhy ban iya karatun hausaba sosai, yana bani wahala”. Ido yad'an zaro waje, yace, “saboda mi? Keba bahaushiya bacene?”. “bahausa mana”. ‘tafad'a cikin turo bani irinnan ta6ararru’. Baki ya ta6e yana kama hanyar fita, “zaki cigaba da kad'aicinki ashe kuwa”. Ganin zai fice da sauri tace, “please ka siyo zan fara koya to”. “it's better”. ‘yafad'a yana ficewarsa’. Saman gadon ta fad'a ta fashe da kuma mai ban tausayi. Duk abinda ke faruwa Galadima najin komai ta waya, Munaya ma na zauna a sofa har yanzu tana satar kallonsa, amma batajin miyake saurare da ya nutsu haka. Cire wayar yafara k'ok'arin yi ya jiyo muryar Nuren na fad'in “hello brother kana jina?”. Galadima yace, “eh”. “okay duk kaji aimi ta fad'a ko?”. “duk najiku, saika samin ido akan duk d'unsu, a bincikomin komai daya shafesu”. “indai wannanne insha ALLAH angama, amma ni a ganina banda wannan Shareffuden d'in datace, domin babu wani kamanni a cikin nashi sunan, ballema tace k'anin step mom natane”. “Humm Nuredeen kenan, shifa mak'iyi ba'a rainashi, mutane da yawa sukan d'auki cinnaka ba komaiba, amma idan yacijesu sukan ji cizon har a ransu, dan haka karka ta6a d'aukar mage mafi sauk'i akan kare, itama idan taga nama citakeyi”. “wannan gaskiyane brother, ALLAH yabamu sa'a”. “amin ya rabbi, naji kuna maganar buks da ita, kaje ka samo mata dukkan Wanda take buk'ata, har English novels d'in, sannan ak'ara tanadar mata dukkan abinci mai k'yau datake so”. “insha ALLAH angon Munaya”. Girgiza kai kawai Galadima yayi ya yanke wayar. Kallon Munaya yayi suka had'a ido, saita janye cikeda basarwa. Shima tashi yayi ya koma gaban mirror, duk uzirinsa yayi ya gama sannan yamatsa ga wardrobe ya ciro kayan dayake buk'ata. Ganin haka Munaya tazame ta kwanta cikin kujerar yandama bazata gansaba. Baki kawai ya ta6e yacigaba da saka kayansa. Bayan yagama yamatsa kusada ita, “tashi ki canja kaya ki rakani wani waje”. Fuska Munaya tad'an yatsina, kamar zatace wani Abu saikuma ta yunk'ura zata tashi kawai, hannunta ya kama ya taimaka mata ta tashi zaune. fita yayi abinsa. Hakan yasata fahimtar zai jirata a falo kenan. Bata 6ata lokaciba ta canja kayanta da atanfa skt da riga, takawo after dress ta saka sannan ta nad'a Vail d'in rigar, d'as ta fito itada cikinta, kamar ka saceta ka gudu abinka. Tunda ta fito ya zuba mata idanu, ko k'yaftawa bayayi, saida yaga tana gabda k'arasowa garesa ya basar yana mik'ewa. Gaba yayi tabisa abaya, yandama yake taka steps d'in benen dolene ya birgeka, duk takunsa nakan idonta, yayinda itama take binsa daki-daki a hankali. Babu kowa a falon, dan haka suka fice basu nemi kowanba. A mota yana tuk'i da sauraren karatu itakuma tana latsa waya suna charts a families group d'insu. Sai murmushi take zubawa, duk abinda take yana kallonta ta gefen ido. Sun isa wani k'aton shagon saida kayan babies, duk abinda kake buk'ata zaka sameshi indai na yarane daga 1year zuwa 15. Itadai mamaki ya ishi Munaya, miye nawani kawota nan? yabari a haihun mana ma. Tarba ta musamman aka musu, hakan ya tabbatar ma Munaya yasan mai shagon kenan, dan yanda aketa girmamasu sai abin ke bata mamaki. gashi indiyanci sukeyi bata fahimtar maganganunsu. Itadai tana zaune hankalinta ya rabu gida biyu, wajensu Galadima da kuma wasu mata biyu da yaransu uku dabazasu wuce 7-7years ba, yaran k'yawawa masha ALLAH, ga wayo. Galadima ya juyo zai mata magana saiya lura da inda ta zubama idanu, shima shagala yay a kallon yaran, iyayensu na za6ar kaya amma su suna tibirewa sai Wanda sukeso za'a d'auka. Munaya sai zuba murmushi takeyi, dan suntafi da imaninta, shima murmusawa yayi yana lasar lips, kafin ya d'auke kansa ya maida ga Wanda suke maganar. Zuwa can gardama ta hark'ume tsakanin yaran akan wani game da iyayen ke dubawa maybe zasu saya musu ne. Kuma games d'in suna kusada Munaya ne, d'aya a cikin yaran ya d'akko yazo wajen Munaya yana tambayarta wai “Aunty wannan yafi dad'i aidai ko?”. Munaya bata fahimceshiba, dan yayi maganane da yaren dabata ji, dan haka saitayi murmushi ta tambayesa yanajin English?. Yaron ya d'aga mata kai alamar eh. Ta kuma murmusawa, duk abinda ke faruwa a idon Galadima ne. Da turanci munaya tace, “yarona kai kata6a irin wannan game d'inne?”. Murmushi yamata shima, yace “aunty akwai dad'i ma sosai, ranar saida na cinye kharan a gidansu ma”. “da gaske?”. munaya tafad'a tana dafa kafad'arsa. Kansa ya d'aga mata, cike da d'oki yace, “Aunty na koya miki?”. Munaya ta d'aga masa kai. Game d'in ya d'ora a cinyarta, ya danna wasu Number, sai kuma ya zubasu cikin d'aya, duk suka shige. Cikin mamaki munaya tace “mikenan to?”. Shima dariyarsu ta yara yayi, yace “Aunty ai wayo na miki, Abu guda d'ayane, amma sainayi ammafani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d'aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had'a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d'aya ne na had'aka kuma akan Abu guda d'aya kacal”. Sosai abun ya birge munaya, tayi dariya har hak'oranta na bayyana, jawo yaron tayi a jikinta ta rungume. Iyayensa dake tsaye suna kallonsu tun d'azun duk sukayi dariya suma, sannan suka matsa kusada munaya suna bata hannu alamar gaisuwa. itama ta mik'a musu suka gaisa, d'aya tace sunanta Radha, d'ayar kuma tace Anjali, munaya ta fad'a musu nata suna itama, sannan takamo hannun saran yaran tana tambayarsu suma, d'aya yace vanish, d'ayan kuma Anjun, duk kumatunsu ta sumbata tana sakama rayuwarsu albarka. Wadda tace sunanta Radha tace “kiyi hak'uri da surutun Vishnu shi baya gajiyane ko kad'an”. Munaya tace babu komai. Daganan sukai gaba, munaya tana binsu da kallo tana murmushi, yaran sai waigenta suke suna d'aga mata hannu. Sunje wajen biyan kud'i akace subar kud'insu inji mai shagon, da mamaki suka tambayi wanene? Mikuma yasa ya barmusu. Mai kar6ar kud'i ya murmusawa yana fad'in mijin matarcan da kuka gaisane mai shagon ai. Munaya batasan mike faruwaba taga sun dawo, godiya suka shiga yimata, ta tambayesu akan me?. Suka bata amsa da cewar mijinta bai kar6i kud'in kayansu ba. Murmushi tayi, k'asan ranta tana mamakin dama shagon na Galadima ne?. Sun katse mata tunani da tambayar kozasu samu number ta, babu musu tabasu sukayi sallama suka tafi. Maida kallonta tayi ga Galadima dake zaune yanata latse-latsen laptop tamkar baisan mike faruwaba, da alama yana duba kayane ko wani Abu, dan time to time Wanda yake gefensa yakan nuna masa wani yanki na kayan dake shagon, shikuma ya waiga ya kalla, idan bai hango sosaiba saiya kalla ta cikin Computer d'in dake tareda cctv cameras d'in shagon. Munaya tace kai mutuminnan akwai son kud'in tsiya, kai komai kana saidawa, wata zuciya tace idan bai nemi kud'iba dame zai kula da mahaifinsa?. “hakane kuma”. ta fad'a a fili tana sauke ajiyar zuciya. Kusan mintuna 15 saitaga ya taso ya nufota. Zama yay kujerar kusa da ita yana fad'in “sorry friend na barki ke kad'ai. kin gaji mu tafi ko?”. Munaya tad'an yamutsa fuska tace “ba sosaiba”. Ya d'an murmusa, “ok tunda baki gajiba kozaki d'an mana taimako ni da abin cikin kwan?”. Hararsa tad'anyi, itafa haushin wannan abin cikin kwan dayake fad'a takeji. Hannu yasa ya dafe bakinsa yana fad'in “maida wuk'ar”. A tare suka dinga zagayawa cikin shagon, dayake babbane sosai, kayan yarane kuma zalla a wajen, komai bibbiyu take d'auka, baice komaiba, dan yasan dai bai wuce tana had'awa da cikin 'Yar uwarta Munubiya bane. Sund'an d'iba kaya babu laifi, yabada ATM d'insa aka d'auka harda na wad'ancan matan, yaran shagonne suka kai musu har cikin mota. Yanzuma haka suka taho tamkar kurame. Kowa da abinda yake sak'awa.... Danja data tsayar damune yasakashi juyowa yad'an kalleni, ganin hankalina nakan wasu yara 'yan makaranta dake mota yace, “dama haka kike da son yara?”. Juyowa nayi Na kalleshi, amma saiya d'auke kai tamkar bashine yay maganarba ma. Nima maida kaina nayi ga yaran, a kuma time d'inne muka sami damar barin wajen. Saida muka fara tafiya nabashi amsa da “yalla6ai kenan, waye zaice baison yaro, a duniya babu abinda yafi k'uruciya dad'i”. Kad'an ya juyo yad'an kalleni yana fad'in “really?”. Nima kallon nasa nayi ina fad'in “na tabbata amsarnan kowama zai baka idan ka tambayesa”. Bai kalleniba yanzun kam, hankalinsa naga tuk'insa, yace, “ALLAH ya kawoka duniya lafiya abin cikin kwan”. “shiru namasa bance uffanba”. Har muka isa gida kuma babu Wanda ya sake magana a cikinmu. Saida yay parking motar a harabar gidan sannan ya juyo gareni, ina niyyar bud'ewa Na fita ya ruk'o hannuna. kallonsa nayi da mamaki, yawani ci magani irin babu raininnan, kamar zanyi magana saikuma nayi shiru muka zubama juna ido, kowannenmu zuciyarsa Na bugawa da sauri-sauri. Cikin k'asaitarnan tasa yace, “Addu'a nayi amma jan aji yahanaki amsamin da amin”. Ni dariyama ya bani wai jan aji, hakanne yasakani murmusawa kad'an ina k'ok'arin janye idona daga cikin nasa, amma saiya hanani hakan, nace, “na amsa ai, bakaji bane kawai”. “aiba kurma kika auraba”. Uhm wannan aure ana tak'ama dashi, Na fad'a a raina, a fili kuma nace, “a zuciya Na amsa”. “k'arya haramun, banji wannan sak'onba a tawa zuciyar”. Da mamaki Na waro idanu waje ina fad'in “ban fahimceka ba”. Lips d'insa yad'an ciza da hak'ora yana matsoda fuskarsa dab da tawa, gashi ya sark'eni da idanu nakasa matsawa, d'an yatsansa ya d'ora saitin zuciyata, muryarsa k'asa-k'asa tamkar mai rad'a yace, “zuciyoyi aminan juna sukan kar6i sak'on juna alokacinda d'aya ya aikashi ga d'aya, karki jahilci kanki har yanzu akwai sauran dama”..... Yana gama fad'a ya saki hannuna, tareda bud'e motar ya fice. Galala nabisa da kallo tamkar wata sokuwa, nakasa motsi nakasa fassara zantukansa da ma'anarsu. Tsawon mintunan dahar bayin gidan sungama kwashe kayan da mukazo dasu ban fitoba, bud'ewa naji anyi, hannunsa kawai ya mik'omin alamar nakama Na fito. tamkar sokuwa haka Na d'ora hannun cikin nasa, ya kamoni ahankali Na fito, maimakon ya sakeni saiya jawoni Na shige jikinsa, ya d'ora kansa a dokin wuyana, cikin kunnena yace “wasu bayanan basa buk'atar fassara, ayanda sukazo ahaka ake barinsu, karki zurfafa tunani, dan yana kawo ciwon kai da hana Hutu”. Ya d'ago kaina tareda janye jikinsa yana d'agamin gira da salute d'ina, ya juya zuwa cikin gida. Binsa kawai nakeyi a baya tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki. A falo muka iske duka ahalin gidan, har Momma dazata kwana yau a gida, Abba ne kawai babu, muduka sun birgemu, Dan hira suke ta nishad'i da girmama juna. Dagani harshi gaishesu mukayi, Sauban da Samha dasuka k'arasa da kayanda da bayi suka shigo dasu suka sakko daga samanmu suna mana sannu da zuwa. Ni kad'ai Na amsa, Galadima hannu kawai ya d'aga musu. Momma tace, “kuje ku huta mana”. mik'ewa mukayi duk a kunyace, ina gaba a yanzu yana baya, suduka da kallon sha'awa suka bimu, dad'i da farinciki Na ratsa zukatansu, innarmu harda kwalla suka cika idonta, Wanda ita kad'ai tasan fasaarar kayanta. ★★★★★★★ Da daddare Galadima Na zaune akan sofa ya d'aura k'afafunsa saman teble yana latsa laptop, yayinda Munaya ke zaune a tsakkiyar gado tana karatun wani English novel na Galadima, buk d'in love story ne dan haka taketa faman zabga murmushi, lokaci-lokaci yakan d'ago ido ya kalleta, saboda idan tayi murmushi yakan jiyo sautinsa. Maida kansa yayi, yacigaba da aikinsa dayakeyi akan numbers d'in layin Abba na sirri, kwatsam sai maganar yaron d'azu na shago mai suna Vishnu ta fad'o masa a rai. *_Aunty ai wayo na miki, Abu guda d'aya ne, amma sainayi amfani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d'aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had'a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d'aya ne na had'aka kuma akan Abu guda d'aya kacal._* Saida yakuma maimaita maganar kusan sau uku a ransa, kafin ya kalli Munaya da dukkan hankalinta ke kan Novel, “Friend!”. Ya kirata a nutse. Da “na'am” Na amsa ina kallonsa, saikuma Na janye saboda wandon jikinsa baiko rufe masa cinyaba, sai k'aramar riga mara hannu. Yace, “mikika fahimta ga zancen abokinki na shago?”. “abokina? waye abokina?”. Tasowa yayi dagashi har laptop d'in da coffee d'insa ya hawo gadon, nima saina tashi zaune sosai. Ya zauna ta gefe tareda ajiye mug d'in hannunsa a drowa d'in gefen gadon, laptop d'in kuma a saman gadon d'ayan gefensa. hannu ya mik'amin alamar nazo. Ban musa masaba Na matso, ya kamoni ya sakani a jikinsa, dan tsakkiyar k'afafunsa ya sakani, saina zame Na kwanta na d'ora kaina a cinyarsa, (dama wajen lak'ewa nake nema🤪). Ya kar6i buk d'in hannuna ya ajiye gefe, ya d'ora hannunsa a saman cikina. Kuma maimaita masa tambayar nayi. Ya shafa sajensa yana cije lips, “miyasa wataran kike da basarwa”.. “ni d'in?”. ‘nafad'a ina nuna kaina da kallonsa’. Bai bani amsaba yace “ina nufin yaron d'azun”. “Oh sorry”. nafad'a ina gyara kwanciyat. Nace, “wai Vishnu? ”. Kansa ya d'aga min “to amma wace maganace tasa? tazama abin nazari yalla6ai?”. “game”. “game! game!” nashiga fad'a ina k'ok'arin tunanowa. “okay, wai yanda yafad'i yaci game d'in?”. “Uhhm”. ya fad'a a tak'aice.. Nikuma saina murmusa, “to dukda dai bansan ma'anar d'aukar maganar da muhimmanciba amma anawa tunanin yana nufin _abinnan mabanbantane, amma saiyayi amfani dasu cikin Abu d'aya, kuma sukai masa aiki iri d'aya, sannan duk shi kad'ai ya sarrafasu akan Abu d'aya bawai yayi tarayyar da wasu mutane da yawa bane ko aikinsa had'aka,_ wannan itace fahimta ta ga zancen nasa”. Lumshe ido Galadima yayi, ya duk'o a hankali ya mannamin Sumba mai k'au a goshi. Sannan ya d'akko novel d'in ya damk'amin a hannu, yajawo laptop d'insa yacigaba da aikinsa. Kallon mamaki kawai na zuba masa, kokad'an ban fahimci muhallin maganar tasaba da son fashin bak'i. Batareda ya kalleni ba, idonsa akan system d'insa yace, “kallonfa?”. Janye idona nayi ina ta6e baki. Shima saiya ta6e nasa alamar yaganni kenan. karatuna nacigaba shima yacigaba da aikinsa yana shan coffee time to time. Yayi aiki mai tsawo kafin yasaki wani murmushi da ajiyar zuciya, ya kalli munaya da barci ya kwashe, fuskarta ya shafa yana kuma sakin wani murmushin, “tabbas gaskiya Vishnu ya fad'a, mutum d'ayane ke amfani da Numbers daban-daban wajen kiran Abba munaya, duk wadda yagama da ita bazai sakeba, tagama aikinta, a wannan karon lallai kunyi aiki da basira, wadda harta birkita tunanin Sameer, kuna kiran Abba da mabanbanta Numbers wad'anda kunrigada kun gama shirya matakan da kowacce number bazata sake aikiba, shima kansa ya d'auka mutane daban-dabanne ke kiransa. O ALLAH wannan shine bada k'afa, to ai inkunsan wata bakusan wataba kuma, Muhammad Sameer ruwane, idan bakasha yanzuba zakasha anjima, idan kak'i kuma k'ishirwa ta kasheka. Inhar tarkon dazan d'ana zai d'annu dai-dai, tabbas zan cafke kurayen daji mai duhuwa a wannan karon”. ‘Ya k'are maganar da jan hancin munaya yana kuma sumbatar goshinta’. Kwanciya ya gyara mata sosai, ya ja bargo ya lullu6a mata sannan yaje bayi ya d'auro alwala, kamar yanda ya saba ya raya wannan dare da nafilfili da godiyar ALLAH, kafin yazo ya kwanta gefen munaya zuciyarsa na cike da annashuwa da farinciki, kaikace komai yayi done ne. Addu'a ya musu sannan yasakata jikinsa barci ya Lula dashi shima. Nima mai d'aukar rahoto bara nad'an rintsa my sweet sisters😉🤩......................✍🏻 Duk Wanda yaga ban amsa massage nashiba yamin afuwa, nayi up date WhatsApp d'inane🥰🥰🥰🤝🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu👏🏻😭_* *_typing📲_* *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ___________________________ _jinjinar gaisuwa a gareku da fatan alkairi, Bilyn Abdull ta gaisheku, gaisuwa irin ta musamman d'innan my lovely sister's🥰🥰🥰🥰🥰🤝🏻_ *_Aysha Manshart (Ummu zunnur😍), Hafsa abdulaziz, mmn fukaihat, Hannah A Ali, marnona, Mmn Al'ameen, Sumee waziri, Ummu walid, Yar tulluwa, Khadija Aliyu Sa'id, Umm Abdul, Umm Yusuf, Mrs Ahmad, zubby abdullahi, Hajara Ismail shatu, Ummu barakat, maryam haruna, Ummu sulaym, Ummu Ahmad, Haizarana halliru._* I love you mazga-mazga😂🤸🏻‍♀ ____________________________ ~Book 2~ 👉🏻2⃣0⃣➖2⃣1⃣ ................Tafiyar su Abba dai ta kankama, dan Abba ya matsa ainun, dole Galadima ya musu dukkan shirin daya kamata, zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu jirginsu zai d'aga. Da yake yau Saturday ce babu aiki, amma hakan bai hana zama gidan shiru ba, su Sauban da innarmu sun fitane, nikad'aice a gidan sai jakadiya, nima barci nake suka gudu suka barni a gidan. Yunwar dana farka da ita ta tilastamin sakkowa k'asa neman abinci, dan a 'yan kwanakinnan nazama wata acici, danaci abinci danaji sabuwar yunwa, narasa wannan dalili. Bannemi kukun gidanba ma ko cikin bayi, nahau dafa abinda zaimin saurin dahuwa, kafin ya dahunma saida na d'umama madara nad'ansha sannan 'yar nutsuwa tazomin. ina sauke abincin kuwa Na juyoshi a plate na koma sama. tun a hanya naji k'amshin turarensa, ban kawo yashigo gidan bane nidai na ida hawa. ban tsaya faloba na shige bedroom. Galadima dake zaune a sofa yana kwance igiyar takalminsa ya d'ago ido yana kallona da amsamin sallamar danayi. Sandunan wasan Golf d'insa daya shigo dasu ya zube a carpet d'in gaban gadon na janye gefe na zauna, dan nafijin dad'in xaman k'asan yanzu. Shidai bai fasa kallona ba baikuma bar cire takalman ba, dan abincin dayaga ta zubo yakema kallon mamaki, kafinfa yafita harda kukanta ta farka wai yunwa takeji, haka dole yafita yasaka kuku dafa mata abinci, baibar gidanba saida taci takoma barci, da fitarsa kuwa baifi 3hours ba, amma jita yanzu dawani abincin. Ya janye takalaman daya gama cirewa a gefe ya zubamin ido kawai, dukda abincin nada zafi haka nakecinsa da sauri-sauri. Janye plate d'in yayi daga gabana, fuskarsa babu walwala yace, “waike mike damunki hakane?”. Idona harya fara tara kwalla cikin marairaicewa nace, “dan ALLAH kabani, wlhy yunwa nakeji bata wasaba”. Rasa ma mizaicemin yayi, ya zubamin ido kawai yana kallona. a mamakinsa saiyaga ma ina hawaye, abincin ya tura min yana fad'in “wannan cin naki yayi yawa, gama muje wajen Akash ya dubaki”. Uffan bance masaba, shima bai sake tankawa ba yanufi bathroom, yaja wasu mintuna saigashi ya fito d'aure da towel, kallo d'aya namasa na janye idona, wannan abun nasa yafara damuna, yanzu baijin kunyar yafitomin a duk yanda yaso, ko yana mantawa bashi kad'ai bane a d'akin oho. Shima dai kallonta kawai yakeyi, dan nacinye abincin plate d'in tas, a ransa yace shiyyasa taketa zama k'atuwa, irin wannan ci haka. Oho bansan yanayiba, nidai mik'ewa nayi nashige bathroom abuna, nasamu nai wanka da ruwa mai sanyi dan naji dad'i. lokacin dana fito yagama shiryawa cikin ainahin kayan malam bahaushe, blue d'in shaddace akaima d'inkin wando da 'yar shara, saidai tasha aikin sarauta d'an asali da d'aukar hankali, ya kawo bak'ar hularsa ya d'ora, itama dai irin ta mutanen dace *dara* (irin wadda su ibro suke sawa), saidai wannan batakai waccan tsawoba, dai-dai take kamar sauran huluna. harga ALLAH kwalliyar tasa tamin k'yau, dan yafito a cikakken bahaushensa, turare yake fesawa amma nakasa d'auke idona daga kansa. Duk kallon k'urillar datake masa yana kallonta ta gefen ido, wani miskilin murmushi yayi Na gefen baki, ya juyo muka had'a ido, saurin janyewa nayi cike da basarwa. Shikuma ya ta6e baki yana takowa inda nake. tuni zuciyata harta fara tsitstsinkewa, dan ayanzu babu abinda nake gudu kuma irin yace zai ra6u jikina koya nunan buk'atar wani abu, shima inaga fahimtar hakanne yasa a kwanakinnan bai cika takurani kamar abaya danake kawo kaina ba. Ganin yanda ta tsorata sai abin yabashi mamaki, waskewa yay yafasa zuwa gareta, ganin ya canja hanya Na sauke ajiyar zuciya wadda har fitar sautinta saida yaji. Kansa kawai ya girgiza ya zauna a bakin gado yana fad'in “kishirya mana”. Bance komaiba nawuce Na d'auki Arabian gown da zan saka, dan yanzu sune kawai kayan dakemin dad'in sakawa, bathroom nakoma Na saka, Na fito Na iskeshi yana waya da Akash dake fad'a masa inda zamu iskeshi. wucewa nayi nad'an gyara fuskata, inason shafa mai a k'afa amma ina tunanin yanda zan sunkuya. Lura da yay da hakan yasashi mik'ewa, wajen takalmanmu yanufa ya d'aukamin masu taushi cikin wad'anda ya siyamin saboda naji sauk'in tafiya. Kafad'una ya kama ya zaunar dani ga stool d'in mirror, sannan ya d'auki man ya duk'a k'asa a gabana yakamo k'afata yana shafamin, nidai kallonsa kawai nakeyi, harya gama yasakamin takalman ya d'auran igiyar yana fad'in “yakamata ma mufara fita kina motsa jiki, dan k'afarnan kamar tana d'anyi fushi a kwanakin nan”. Nace, “ai bata ciwo”. Baice komaiba yamik'e yana kama hannuna ya mik'ar dani. A falo muka iske jakadiya tana kallo, tamin sannu sannan ta gaida Galadima. yafad'a mata zamu fita, tabimu da addu'ar dawowa lafiya. Tafiyar tamu takasance shiru kamar yanda muka saba inhar ta had'amu mu biyu, maimakon muje asibiti sai gamu awani gida mai k'yau da tsari, kafin nasamu damar tambayarsa saiga Akash yafito yana zabga murmushi, rungume juna sukayi da Galadima, kafin ya d'ago yanamin sannu da zuwa. Fuskata da murmushi Na amsa masa tareda gaishesa. A tsararren falon gidan muka yada zango, komai ya birgrni dan an tsarashi yanda ya kamata. dandanan Akash ya tara mana kaya a gaba, sannan ya zauna muka sake sabuwar gaisuwa. Suka d'ora da barkwancinsu irin Na abokan da suka shak'u. A firar tasune nakejin Auren Akash d'in ya matso, dan zasuyi baiko next week da wadda zai aura, Na tayashi murna da fatan kaiwa da rai. ya amsamin bakinsa har kunne. Bayanin yawan cin abincina Galadima yamasa, Akash yay dariya, “to inbanda abinka Sameer ai dole taci abinci fiyeda da, karka manta yanzu ba ita kad'ai bace, kuma saitaci abin cikinta zai samu shima, kunk'i yarda ayi scanning muga adadin 'ya'yan namu ko jinsun su”. galadima ya murmusa kawai, karka damu, miye Na zazzari, kwana nawane insha ALLAH zaizo ko zatazo duniya, yanzu dai tunda ba Matsala bane cin abincin ai Alhamdllh”. “no babu wata Matsala, abindama yasa zakuga yanzu takanyi saurin jin yunwa cikinta ya tsufa, shima yak'ara girma abin cikin nata, dan zama ta dingajin idan bataciba ana motsi da harbe-harbe a cikin, idan da zaka kalli cikin a time d'in datakejin yunwar sosai har yanda yake wuntsilniya saika gani kaima, Madam ko hakan baya faruwa?”. Nace, “yana faruwa sosai, amma da zaran naci abincin sai a nutsu”. Akash yay dariya, “Alamun yana cikin k'oshin lafiya kenan, abincinne kawai buk'atarsa”. Galadima ya juyo muka kalli juna, gira ya d'agamin nikuma nayi murmushi ina kauda idona gefe. Daga nan wata hirar suka koma, wadda nake zargin akan Abba nane, dan naji Akash Na fad'in doctor Johnson yabama Abba glasses d'in amatsayin medical glasses, kuma ya gargad'esa karyayi wasa dashi saboda jijiyar idonsa nason samun Matsala, to sunason glasses d'in yazama riga kafine, dayake da turanci suke magana sai yazam inaji nima. Murmushi Galadima yayi yana jinjina kai. A raina nace mikuma Galadima ya shiryama Abban?. banida mai bani amsa, dan haka nayi gum. Muna niyyar tashi Akash yace bamu isaba, bazamu tafi bamuci komai a gidansa ba, kodan munga bashida matane. Badan munsoba mukad'anci abinda zamu iya, sannan yayo mana rakiya har wajen mota. Saida munaya tashiga mota sannan Galadima ke fad'ama Akash yayi mantuwa. Akash yace “tami?”. Babu kunya Galadima yad'an ciza lips yana tambayar Akash wai miyasa yanzu take gudunsa?. Akash yabashi amsa da maybe salon cikine, danshi babu yanda baya zuwa ma mace, wani yasata sha'awa wani kuma akasin hakan, amma idan na haihu zan iya komawa normal. Galadima ya basa hannu sukai musabaha sannan ya shigo mota yana masa godiya. Tunda muka fara tafiya saina kasa jurewa, na jeho masa tambaya muryata a sanyaye. Kad'an ya juyo ya kalleni ya maida kansa ga tuk'i, saida yaja wasu mintuna kafin yasaki ajiyar zuciya tareda cizar lips nashi, batareda Yakuma kallonna ba yace, “Friend! Wani karatun baya buk'atar fashin bak'i, akan karantashine a barsa a yanda yazo”. Murmushi nayi ina maida hankalina gareshi, nace “yalla6ai koda shi wannan karatun zai iya fita a jarabawa?”. “Humm” yafad'a yana rage gudun motar, yanzunma bai kalleniba, yad'an zakud'a jikin sitiyarin sosai, “sometimes akanyi burin cin jarabawane domin canjin aji ko gama makaranta ko shiga, saidai awannan karon ni nawa jarabawar da banbance-banbance tazo, dan bana buk'atar cin jarabawar kai tsaye, har sai harsashina ya isa ga zukatan malaman”. “to amma yalla6ai karka manta Hasashefa ba shi bane yak'ini”. “wannan gaskiyane yalla6iya. Saidai yak'ini kuma baya amsa sunan tabbaci, daga lokacinda kika shiga fili wasa kika saka aranki bazakiyi nasara ba, to da kamar wahala kiyi nasarar, duk abinda zanyi nakan rok'i ubangiji nasara Kafin yinsa, sannan na cika zuciyata da kwad'aituwar samun wannan abin, lokuta da dama mutane kan Gaza tsarkake zuciya kafin su cikata da buruka, shiyyasa kikaga duk gudun jirgi a samaniya wataran gaggawa nasakashi tarwatsa a filinda ba muhallin saukarsaba, kiringa zama mai yak'ini saikiga kin tabbata a jerin masu samu”. Murmushi nayi har hak'orana na bayya, nace, “dakai kanarine danace kafi dukkan halittar kanari iya raira zance, dakuwa mawak'ine saina saka a jerin masu zak'ak'an murya, inkuwa a Marubuci kazo to tabbas kai Kanada yawan fik'ira, domin hikayarka zata yawaita saye zukatan mabiyanka ne”. Gefen hanya ya gangara, ya kashe motarma baki d'aya ya maido hankalisa gareni. “Munaaya!” yakirani cikin wani yanayi kuma murya ahankali. nima saina amsa masa a sanyaye. Hannuna ya kamo cikin nasa yana mirza yatsun a hankali, yaci gaba da fad'in “A shekarun baya ni mutumne mai ra'ayin Kansa, ma'ana murd'ad'd'e mai wahalar sha'ani, sannan mai zama a bisa tsarinsa, kece mutum ta farko dana fara doguwar magana da ita koda bana so, nakanyi mamaki a duk lokacin da kika taya nazamo mai sallama miki, anya kuwa bakizo da wani Siddabaru ba?”. Idanu nad'an fiddo waje, nace “siddabaru kuma yalla6ai? to ai awajena ni har gobe kana akan wad'annan ra'ayoyin naka, dan banga canjin dakake hasashen kasamu ba, amma miyasa kace hakan?”. Numfashi ya sauke ahankali, kafin ya ciji gefen lips nashi yana Sosa girarsa d'aya da d'an yatsa “wannan sak'on zuciyane, kibata dama, zata tabbatar miki da cewar wannan Muhammad Sameer d'in yasha banban dana shekarun baya”. “sak'on zuciya kuma?”. nafad'a cikin hasashe, dan nikam Yakuma dilmiyar dani. Mortar ya tada yana fad'in “well basai kin zurfafa ba, dan haryanzu akwai sauran dama”. Baki na d'an ta6e ina gyara zama, “har walau zancen “dama! dama! dai again?, bana son saka baki a hurumin daba nawaba, amma abinda nasani dama dai duk damace, sannan mai ita yakan tanadar mata dukkan muhalin daya tadace da ita, damarmu ce mu damata takowane hanya mukaso”. Idanunsa ya lumshe yana sakin wani k'asaitaccen murmushi daba koyaushe yake irinsaba. Jin Sautin murmushin ya sakani juyawa na kallesa, ya d'agamin gira yana maida hankalinsa ga tuk'insa. Babu Wanda yasake yin magana har muka Isa gida. har yanzu babu Wanda ya dawo, dan haka muka haye sama kai tsaye. dama na k'agara na cire rigar jikina saboda azababbiyar zufar danakeji, danma ya tausaya min yad'an saka AC a mota, ban iya zama ba saida na watsa ruwa, nifa abubuwan sunmin yawa, nice jin zafi nice ci kamar gara, harda alwala nayo, Dan magriba tayi. Ina fitowa shima yashiga yayo alwala. Koda yafito saiya wuce masallaci. Ina jiyo hayaniyar su Samha dasuka dawo amma nakasa sauka, ina kwance abina, hawa da saukarnan bak'aramin wahal dani yakeba yanzu, ahaka Galadima yadawo ya iskeni, sallamarsa kawai na amsa, amma ban iya d'agowa na kalleshiba. Saida ya sauya kayan jikinsa zuwa marasa nauyi kafin yazo ya zauna kan sofa yana fad'in “lafiya dai?”. d'ago ido nai namasa d'an murmushi, nace, “babu komai, gajiya ce kawai”. Shima murmushin yamin, cikin lumshe ido yace, “Sorry friend, saura k'iris insha ALLAH”. “Humm” kawai nafad'a batare da nace masa komaiba. Daga nan muka d'anyi shiru, kusan mintuna 3 yanata latse-latsen wayarsa, batareda ya kalleni ba yace, “Abba kuwa yana saka zobe?”. Kallonsa nayi, amma hakan baisa ya kalleniba, a d'arare nace, “eh yana sakawa amma miyasa kamin wannan tambayar?”. Wayar ya ajiye yana sauke ajiyar zuciya, ya saka d'an yatsansa yana bubbuga la66ansa ahankali, yayinda idonsa yake a kaina tamkar mai nazari, “kina ganin idan kika bashi zai saka?”. Yunk'urawa nai na tashi zaune sosai, “dan sakawa zai saka, amma kana ganin bazai zargi wani abuba kuwa?”. “miyasa kikace haka?”. Shiru nad'anyi, dan ganin ina neman zirma kaina, saina d'an murmusa kawai cikin basarwa, nace, “waynot abashi ba kai tsayeba”.. Murmushin gefen baki yayi, yace, “y'ar tsuntsuwata wai mikike tunanine? da har kiketa kwana-kwana haka?”. Baki na tunzuro gaba, ina fad'in “nidai ba tsuntsuwa bace ba”. Dariyace ta kufce masa babu shiri, yasaka hannu yana rufe bakinsa. Haushi ya kamani na d'auki filon dana kwanta na jefa masa. da sauri ya cafe yana cigaba da dariyarsa, hakan yasa najawo na kujerar ina cigaba da kai masa duka yana karewa da wancan. daga k'arshe sakkowa yay yahad'a nida filon ya rik'e yana fad'in “sorry sorry na bari, ba 'yar tsuntsuwa ba giwar mata”. Hararsa nayi nafara kukan shagwa6a kuma. dariya Yakuma sakawa yana fad'in “toni bansan mikikeso nace mikiba kuma?”. “ni banaso duka”. “to shikenan nabari, yanzu dai yaza'ayi Ring yaje yatsan Abbanmu to?”. ‘yay maganar yana d'ora kaina jikin kafad'arsa’. “saika fad'amin sirrin sannan zan fad'a nima”. Ya murmusa yana jan hancina, “kin cika wayo yarinyarnan wlhy”. K'aramar dariya nayi nace, “ai awajenka na koya”. Murmushi kawai yay baice komaiba, ya jawo wata 'yar k'aramar bag mai k'yau fara ya mik'omin. Kar6a nayi ina tashi zaune sosai na bud'e jakkar ina fiddo kayan ciki, agogone mai masifar k'yau da tsari, na azurfa 'yar asali mai tsada, sai wani d'an akwati da ring mai k'yau na azurfa shima, an masa ado da farin stone mai garai-garai tamkar diamond, na jujjuya zoben kafin na d'ago mu kalli juna ni da Galadima, ido d'aya ya kashemin😉. Janye idanuna nayi nakuma maidawa ga zoben ina k'ok'arin sakashi a yatsana, saidai yamin yawa sosai, na cire ina fad'in “amma gaskiya zobenan ya had'u sosai yalla6ai”. “duk haduwarsa bai kaikiba ai”. ‘yay maganar acikin kunnena’. Kallonsa nayi, amma saiya basar tamkar bashi yay maganar ba. Lips na cije na d'an hararesa. Shikuma ya ta6e baki. Na maida kayan duk a cikin bag d'in dad'an hanzari ina rik'e cikina dayay wata wuntsulawa. “lafiya?”. ya fad'a yana rik'o hannuna. 'Dagowa nayi na kallesa da k'yar, da hannu na nuna masa cikina dake juyamin, jinake kamar numfashine zai bar jikina. Babu shiri ya dire wayar hannunsa ya rik'oni jikinsa da k'yau. Sosai na fara murk'ususu ina kuka da k'ank'amesa, dukya rikice, yama rasa mi zaiyi?. Ana cikin haka saiga sallamar Aunty Mimi dataga shirun yayi yawa sun dawo ban sakkoba, saitai tunanin kobana jin dad'ine, sallama tayi Galadima ya amsa murya a rikice, hakanne yasakata shigowa batareda jiran isoba. Da hanzarinta ta k'araso tana tambayar miya faru?. nidai kuka kawai nake ina kuma k'ank'ame Galadima. Shine yasamu damar mata bayani sama-sama, yak'are maganar da fad'in “Aunty mutafi asibiti please, maybe haihuwa Ce?”. Da sauri tace, “badai haihuwaba Sameer, cikin dake wata takwas, kaga ina zuwa”. Ta fita a hanzarce. Babu dad'ewa sai gata tadawo da innarmu da jakadiya, dak'yar innarmu ta amince ta hawo, danma taga tsantsar rikicewar da aunty Mimi tayine. har yanzu dai kukan nake ina jikin Galadima dashima dukya koma kalar tausayi kamar zaiyi kukan. Ganinsu a haka yasaka innarsu munaya k'ok'arin komawa da baya, dan saitaji kunya ta kamata, dukda tasan suma bada son ransuba ne. ita kanta jakadiya taji kunya. ganin innarsu munaya zata gudu Aunty Mimi tayi azamar rik'o hannunta. “please inna karki duba ta kunya, halen datake cikine abin dubawa, kowa yasan dai ba haihuwa baceba tunda da saura”. Ajiyar zuciya inna ta sauke, batare da ta motsa daga inda takeba takuma musu kallo d'aya ta d'auke kanta, tace, “inaga juyine ai, zai lafa insha ALLAH”. ‘tana gama fad'a ta fice abinta’. Jakadiya da aunty Mimi suka kalli juna, murmushi jakadiya tayi, tace, “gaskiya ta fad'a, juyine, amma nadad'e banga uwa mai kawaiciba irinta a wannan zamanin”. Murmushin itama aunty Mimi tayi, ta maida kalonta kansu, yafara lafawa sosai, dan haka munaya tafara tsagaitawa da kukan. Galadima yakuma k'ank'ameni a jikinsa sosai yana shafa kaina, nikam sai ajiyar zuciya nake saukewa tareda shashshekar kuka, ya manna min kisses a kaina idonsa a lumshe, danshi yama manta dasu Aunty Mimi a d'akin. Jakadiya ma dai lalla6awa tai ta gudu, dan taga magajin gari yau sai a hankali. Aunty Mimi ta tako inda suke ta zauna a sofa tana fad'in “sannu Munaya”. Bud'e ido Galadima yayi, harsun kad'a zuwa launin jaa, yad'an furzar da iska yana lek'a fuskarta, barci ya d'auketa. ido ya d'ago yana kallon aunty Mimi dake kallonsu cike da sha'awa, tamasa murmushin kwantar da hankali, ajiyar zuciya ya sauke yana cije lips da jinjina mata kai. Tace, “tayi barcine?”. Nanma kansa ya jinjina mata, yana gyarama Munaya kwanciya a k'irjinsa yanda zataji dad'i, yace, “Aunty Mimi amma yakamata muje asibiti aga miye matsalar?”. “karka damu my k'ani, juyine kawai, insha ALLAH babu wata damuwa. bara inje nima saida safe, idan kuma kaga dawata matsala saika kirani muje asibitin tunkan dare ya kumayi”. Bayan fitar aunty Mimi kuma k'ank'ameta yayi yanamai jin tausayinta na ratsashi, ya sumbaci goshinta, kafin ya d'auketa dukda nauyin datayi ya maidata saman gadon, yanzunma a jikinsa ya sakata, yaja bargo ya lullu6esu tareda musu addu'ar kwanciya. Cikin barci ta farka da wata matsananciyar yunwa, k'irjin Galadima na shiga girgizawa ina kuka. Galadima ya farka a firgice yana rik'e hannunna, ya yunk'ura da k'yar ya tashi zaune, “miya faru?”. ‘yafad'a cikin muryar barci’. “yunwa yalla6ai, abinci xanci, kafad'a masa magana yabar halbina”. Dukda tabashi tausayi saida ya murmusa, sauka yay yafita, k'asa ya sauka zuwa kitchen, yau saiga Galadima a kitchen🤣, rasa mizaimayi yayi, ganin yana 6ata lokacine kawai dan ba iya uwar komai yayiba saiya fice, dole yaje ya tado kukunsu. Mai aiki da aikinsa dannan saigashi ya had'a mata Abu mai sauk'i, Galadima ya kar6a da kansa Yakoma saman. Isketa yayi zaune tsakkiyar gado tana kuma rurus, saita k'ara bashi tausayi, ya haye gadon da abincin, da kansa yabata yana lallashi. saida tayi nak sannan ya sauka da tiren yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Nikam hankalinna kwance nazame na kwanta, barci ya sake kwasheni. Mamaki yasakashi tasata gaba yana kallo, saikace wata mai aljanu, lallai duk namijin daya kasa tausayawa matarsa lokacin da ciki yake jikinta yacika mara tausayi number d'aya, babu abinda miji zai iya biyan matarsa dashi akan rainon cikinsa datayi da tarbiyyar 'ya'yansa, amma a wannan time d'in wani namijinma rashin tausayinsa ke tashi akan matar, ALLAH ya ganar dasu to. Amin galadima🙁😔. ********************** Washe gari A safiyar yau su Abba suka tashi da shirin komawa Nigeria, gaba d'aya saina tashi duk babu dad'i, jinake kamar karsu tafi, dana tuna yaune zasu barmu sai hawaye ya zubomin, inama zai amince nidai nabisu mu tafi tare?. Agogo da zoben jiya na d'auka nafita masaukin su Abba, dan Galadima ya fita tunda sasaafe, bansan ina yajeba. Saida nayi sallama aka bani izinin Shiga sannan na shiga, Abba na zaune a bakin gado agogo rik'e a hannunsa suna magana da innarmu dake tsaye ita kuma tana zuba sauran kayansu a k'aramin akwati. Abba yay murmushi yana fad'in “sannu munaya kinji”. Murmushi nayi a kunyace, na dafa gadon zan durk'usa k'asa na gaidasu amma saiya dakatar dani ta hanyar rik'e hannuna, “kinga zauna, inake ina durk'uso yanzu”. da taimakon Abba na zauna a kujerar dake kusada gadon, sai faman jeran sannu yakeyi, nikuma ina amsawa cikeda jin kunya. gaishesu nayi, suka tambayeni yaya jikin? na amsa da “Alhmdllh”. Jakar hannuna na mik'ama Abba, ya amsa yana fad'in “minene kuma?”. “Abba ka bud'e to”. ‘nayi maganar a shagwa6e’. Dariya yayi yana k'ok'arin bud'ewa, “yanzu dai fitinarki k'aruwa ma tayi Munaya”. Innarmu dake ta6e baki tace, “ai bamaka san fitinarta ta zarce tadaba sai jiya, juyi kawai ta zauna tana rusama mutane kuka a gidannan, yo ke aibama asan abin fad'in dazaki bariba ranar haihuwar?”.. “babu abin fad'in dazata bari insha ALLAHU”. cewar Abba yana juya agogon fuskarsa d'auke da murmushi. Nima sai ban kula zancen Innarmu ba nace, “Abba yayi k'yau?”. “sosai kuwa Munaya”. “Abba kawo na saka maka to”. “to amma kekuwa ina kika samu kud'in sayen wannan agogon da zoben mai tsada haka?”. Murmushin nayi, nace, “Abba awani shago mukaje sayen kaya tun kwanaki dashi, daga nace agogon yamin k'yau shinefa yace na d'auka to”. “Amma munaya yayi tsada da yawa, karna sakejin irin haka, dan takurawace ai, idan kuma bashida k'arfin siyen abunfa? Karki sake kinji ko?”. “inasha ALLAHU Abba bazan sakeba, amma dan ALLAH karkace bazaka kar6i wannanba, dan shima bazaiji dad'iba”. Murmushin Abba yayi, yashiga sanya albarka a garemu da abinda ke cikina, hardama addu'ar d'orewar lafiya ga Abie shima. cikeda d'oki naita amsawa da amin, da kaina na saka masa agogon da zoben. Daga nan muka d'an ta6a hira. Dan akwai sauran time sosai na tafiyarsu. Mun dad'e muna hira, dan ko break fast yau tare dasu na sakeyi, dama tun asuba ni yanzu nakeyin nawa🤭, sanda kowa zai k'ara sainayi na biyu.😂 Galadima ma daya dawo ya kimtsa nan yazo ya samemu, yanda suke sakin jiki da juna shida Abba abin na bani mamaki, Galadima yakuma yima Abba bayani sosai akan yanda zaicigaba da tattalin lafiyarsa da kulawa da dukkan dokokin da sukai masa, daga nan muka cigaba dad'an ta6a hira, itadai Innarmu duk adabaibaye take, danma taga yau zasu wuce da bazata zaunaba. Wajen 12pm mukabar gidan zuwa asibiti, a asibitine akayi dogon zama, dan godiya ta musammance tashiga tsakanin surukan guda biyu, Abba kuma yay alk'awarin kuma tsayawa wajen dagewa da addu'oi na musaman ga jikin Abie da alk'awarin kawo wasu taimakon na tsarin jiki, dan sunga fa'idar addu'a sosai. Kowa jiyake tamkar karsu tafi, saboda shak'uwace ta musamman tashiga tsakanin wad'annan families guda biyu, zaman mutunta juna ya gudana sosai a tsakani. Kuka na shiga rairawa lokacin danaga tafiyarfa da gaske yinta za'ayi, sai alokacin muka san ashe wai harda Sauban, zai rakasu saudiyya suyi umrah ta kwana 10, daga nan saisu wuce shikuma yadawo. na kama hannun Abba na rik'e gam nak'i saki zai hau jirgi, su Sauban suka tasani da dariya kuwa, oho ban kulasu ba, Galadima ya girgiza kaiwai yana murmushi, yarinyarnan ta6ararta tayi yawa, yafad'a yana takowa inda muke da Abba yana lallashina. A Kallonsa Abba yayi sukayi murmushi, Abba ya zame hannunsa a hankali yajuya zuwa ga jirgi, yunk'urin binsa nayi Galadima yay azamar rik'o min hannu batareda yayi magana ba, juyowa nayi na fad'a k'irjinsa ina kuma sakin sabon kuka. Hannu biyu ya saka ya rungumoni yana guntun murmushi. Innarmu dake hangenmu ta cikin jirgi ta share hawayenta itama tana murmushi, banda aure waya isa ya rabaka da 'ya'yanka. Abba daya zauna kusada ita ya saka hannunta cikin nasa yana murzawa, juyowa tayi ta kallesa, yamata murmushi yana share mata hawayen da har yanzu sun kasa tsayawa, jikin kafad'arsa ta d'ora kanta kawai. Sauban dake kallonsu yay murmushi, lallai Aunty gimbiya 'yar gatace a gidansu. Saida naji alamun jirgi zai tashi sannan na d'ago kaina, inaji ina gani jirgin yafara shawagi a samaniya harya shilla da iyayena. A motama haka naita sharar hawaye, dayake dagani sai shi da Samha a motar, cankuma Aunty Mimi da Khaleel da jakadiya. Samha tana ta bani hak'uri, amma tamkar tana zuganine, saida Galadima ya harareta yana mata alamar tamasa shiru sannan tayi shiru, shikam ko sau d'aya baicemin uffanba.. Asibiti muka koma, tunda muka shigo Momma ta taso ta rungumeni a jikinta tana lallashi. Galadima ya jingina da bango ya hard'e hannayensa yana kallonmu, a haka sauran suka shigo suka iskemu, Abie ma kallonmu yakeyi cike da tausayina. Saida nasamu na tsagaita da kukan sannan nacema Momma zanci abinci. Galadima yaje kusada Abie ya zauna yana k'aramar dariya, “dama kice yunwa kikeji kika zauna kinama mutane ta6ara?”. Hararsa Momma tayi tana masa dak'uwa, hakama Abie, aunty Mimi kam saida ta rankwasheshi akai. Gurin ya dafe yana fad'in “a'a yazaku tararmin ne kuma?, gaskiyafa na fad'a ko Samha?”. Samha tace, “Uncle nima dai ina bayan aunty gimbiya”. Idanu ya kwalalo alamar tak'aremin. Muka had'a ido na hararaesa. Lips d'insa ya ciza yanamin alamar zan kamakine da ido. Na ta6e bakina nikuma. Dolenesa yatashi yanemomin abinda zanci. ★★★★★★★★★★ Tunda su Abba suka tafi lafiya tamin k'aranci, bana iya tsinanama kaina komai sai kwanciya, dukna fita hayyacina na canja kamanni, ga cikifa sai kuma bud'ewa yake yana k'ara girma. Kai kace ba halitta d'aya bane a cikinsa. Galadima dole ya d'auki hutu a office, idan abinda yazama dolene saiyaje Office kam yakanyi shine ta yanar gizo. Gakuma nasarar jikin Abie daketa k'ara k'yau, dan wasu sassan jikinsa suna nuna alamun fara aiki kamar yanda doctors d'insa suka sanar mana. A kwana na 8 da tafiyarsu Innarmu ranar a asibiti na kwana, saboda jiki dai yak'i dad'i, ga masifaffen cin abinci abin babu arzik'i. ★★★★★★★ Su Abba sun gudanar da ibadar Umrah cikin kwanciyar hankali da nutsuwa, ga Sauban dake nuna musu komai yanda bazasu wahala ba. Suna cika kwanaki goma yasakasu a jirgi suka nufi k'asar haihuwa Nigeria kenan, sun rabu cikeda kewar juna suna saka masa albarka. Sun isa Nigeria batareda sanin kowa namuba sai Yaa marwan da Galadima yakira ya sanarma yaje ya d'aukesu a airport. Isowarsu gidanmu tazama a bazata, hakan yasaka gidan rikicewa da murna, dukda kishin daya cika matan gidan ganin innarsu munaya takoma wata d'anya shakaf saboda Hutu da canji wajen zama data samu, dandanan 'yan anguwa suka shiga shigowa taya murna dama Abba jajen ALLAH ya kiyaye gaba. Innaro babu kunya taketa haba-haba da d'anta, kota innarsu munaya batayi, dan haushinta takeji taje ta zauna a India itako an maidota gida. (Babu mai iyama Innaro dai sai ALLAH🤦🏻‍♀🤣). Su Ayusher da sukazo suka zage suka gyarama inna d'akinta, komai ya koma need, tamkar ba shineba ya had'a uban datti na tashin hankali. Tafiyarsu Abba Nigeria da kwana 5 Sauban ma ya dawo India, ya iske ina asibiti, dan gado suka bani dole, babu ranar sallama ma, k'ila saina haihu. Saidai randa mukayi waya da Munubiya nake fad'a mata tace ai gidama yakamata na dawo na haihu, itama batada lafiyar sosai. Da to na amsa mata kawai, amma ina tunanin yanda Galadima da ahalinsa zasu amince da zuwana haihuwa Nigeria, kuma tunda 'Yar uwata ta ambata dolene hakan za'ayi, kona so koban soba kuwa. ___________________________ *_Two months ogo_*😬🤭 Watanni biyu kenan da tafiyarsu Abba, tunda sukatafi kuma babu wani Abu mara k'yau kona Sosa zuciya dayay gamo dashi, harma ya koma wajen aikinsa hankali kwance. Jama'ar gidansu Munaya kuwa sunyi haushin da nuna hassadar ga inna harsun gaji sun bari, dan sudai san ba kulasu zatayiba, ita yanzu babbar damuwarta ma 'ya'yanta su sauka lafiya, dansu Safara'u duksun haihu sukam, kuma dab da dab sukaita kancamo 'ya'yan, ayanzu haka sunan d'an Fauziyyane kawai yarage gobe idan ALLAH ya kaimu, dan itace k'arshen haihuwa.. Su fiddausi duk suna gida sunzo wanka, iyayensu kowa ta zuba k'arya a hidimar sunan 'yarta, yanzu maman Fauziyya da innarsu munaya kawai aka zubama ido aga yanda zasuyi nasu. Inna dai bata d'ad'ara kanta da k'asaba, iya abinda ALLAH ya hore mata iya shine tai k'udiri yi a hidamar sunansu Munubiya idan sun haihu. Fatantama su sauka lafiyar, dan gasu suna neman share watanni na goma haihuwa babu amo babu labari. Mama Rabi'a cema kawai keta k'ok'arin ta na ganin sun tanadi dukkan abin fita kunya, sai Aunty Salamah dake taimaka musu, wadda a yanzu tazama 'Yar uwa agaresu makusanciya, dan komai nasu tana tsaye a akai tsakaninta ga ALLAH. WASHE GARI akasha sunan d'an Fauziyya. Wanda mijinta da mamarta suka bada mamaki, masu shirin asha kunya sai aka barsu su dajin kunyar da shak'ar bak'inciki irinna masu hassada. Itama tamkar su Haleematu gida ta taho wankan jego. ************************** A wata ranar talata datai dai-dai da cikar cikunanmu wata goma da sati biyu natashi da matsanancin ciwo, Wanda ya rikita Galadima da ahalinsa, nan take doctors sukace haihuwace, aka fara shirin kar6arta amma ina, gadai haihuwar gadan-gadan da gaske amma kuma nagagara haihuwar har washe garin laraba. Nayi masifar galabaita, Galadima yace sumin cs idan bazan iya haihuwa da kaina ba. Amma sukace zan iya haihuwa. Ranar laraba da daddare Galadima da Momma na kusadani suna ta tofamin addu'a saboda zufar danakeyi, nace su kiramin munubiya, babu musu Galadima ya kira Yaa marwan. Shima dakaji muryarsa zakasan a rikice yake, hakan yasaka Galadima tambayarsa ko lafiya?. Yaa Marwan yace, “dadai sauki ranka ya dad'e, tun daren jiya Munubiya ke nak'uda amma haihuwa shiru, sai sunan Munaya kawai taketa kira”. Mik'ewa Galadima yayi tsaye, yace, “muma ai halin da ake ciki kenan, yanzuma itace tace akira mata ita, please kakai mata wayar”. “ok”. Yaa marwan ya amsa yana nufar d'akinda Munubiya take...............✍🏻 Barkanmu da dawowa.🤩✋🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _________________________ *_HASKE WRITERS...._* _gaisuwarku ta musammance, alkairin ALLAH ya baibayeku aminan kwarai abokan tafiya👍🏻😽._ I love you manya-manya fa🥰🥰🥰🥰🤩🤸🏻‍♀ ________________________ ~book 2~👉🏻2⃣2⃣ ................Cikin kuka Munubiya tace, “y'ar uwata ki taho gida please”. Munaya dake saurarenta ta share nata hawayen itama, “insha ALLAH zan taho, ki kwantar da hankalinki, daga yau zuwa gobe ko yaushe zaki iya ganina sweetheart”. Daga haka munaya ta mik'ama Galadima wayar tana cigaba da share hawaye. Hankalinsa atashe yace, “miyasa zakimata alk'awarin zuwa? bayan kinsan ga halin da kike a ciki”. “kayi hak'uri yalla6ai, gara ka barni Na tafi shine mafi a'ala, tun farko y'ar uwata bata 6oyeminba ta sanarmin naje gida Na haihu, idanma baka kainiba to wahala kawai zanta sha anan d'in tunda hakan take buk'ata”. Galadima jiyay tamkar ya make Munaya, ya haukace mata da masifa kaikace zai cinyeta d'anya, “wannan ai canfin banzane da wofi, ALLAH shine kawai maiyi ai bawani alk'awarinku ba, shin Ku bazaku tausayama kanku baneba? yaufa kwannanki biyu kina wahalarnan, wane irin taurinkai ne wannan.......?”. Dakatar dashi Momma tayi ta hanyar d'aga masa hannu, ta dafa k'afad'ar munaya dake kuka tana fad'in “y'ata dama kinmata alk'awarin zakije Nigeria ki haihu ne?”. “Momma ba alk'awari namataba, amma kusan 2months kenan tacemin gida zanzo Na haihu ko? nikuma bance mata komaiba”. Murmushi Momma tayi, ta kalli Galadima dake tsaye yanata kumbura dan haushi. “Muh'd anemi ticket d'in Nigeria yanzunnan”. Da sauri yace “Momma amma......” Hannu ta d'aga masa alamar bata buk'atar jin komai. ya had'iye wani k'ullutu daya tsaya masa a mak'oshi, shifa ba tafiyar tata bace matsalarsa, shima akwai tashi manufar da dalili, amma bashida ikon yin jayayya da Momma, waya ya zaro a aljihu. Ya lalubo wata number yay kira, ficewa yay daga d'akin. Momma tacigaba da lallashin Munaya daketa hawaye, ga zufa Na cigaba da jik'eta dukda AC dake aiki a d'akin. Kusan mintuna talatin Galadima yashigo shida doctor, dannan aka shirya Munaya, nurses biyu suka kaita mota. Wannan karon harda Momma rakkiya Airport, tanata jerama Munaya addu'oi har suka isa. Haka sukai wannan tafiya babu shiri, Galadima kayan tun safenema a jikinsa bai ko koma gida ya canjaba, hakama aunty Mimi. A jirgi yana rungume da ita tanata murk'ususu idan abin ya motsa, wai danma waje Na musamman aka basu dankarta takura. idan nak'udar ta lafa sai barci mai dad'i ya kwasheta, da abin yamotsa kuma tata kuka kenan tana k'ank'amesa, dukta jimasa ciwo da farce, shikam tausayinta dukya cika zuciyarsa. Yaa marwan ma cikin haushi yakira inna ya gaya mata abinda Munubiya tayi, inna taita fad'a tamkar zata ari baki, itada ta haifi su munaya ita tasan halin kowa acikinsu, tabbas a fili Munaya tafi Munubiya fad'a, amma a bad'ini Munubiya tanada ak'idar tsiya da tsatstsauran ra'ayi, lokuta da dama idan takafe akan Abu bata tankwaruwa, kuma dolene Munaya ta amince ayi kokuwa tasha wahala, dan idan Munubiya ta murd'e abin bazai ta6a ya yuwuba saidai idan Ubangiji ya juna mata ikonsa, to amma bata ta6a zaton shirmen nasu zai iya ta6a har lafiyarsu irin hakaba. Dole inna tashirya zuwa asibitin da kanta, taita zubama Munubiya dake fama da kanta fad'a, su mama Rabi'a da Maman Fauziyya sunata bata hak'uri, tunda dai anrigada an aikata, saidai kuma a kiyaye nagaba. Su Munaya sun iso Nigeria lokacin tsakkiyar ranane anan, dan irin 1pm d'innan ne, dayake yakira su sarkin mota ya sanar dasu time d'in dazasu iya isowa, tun wajen 11am ma suna airport d'in.. Tunda Galadima yafara sakkowa daga matakalar jirgin rungume da Munaya akan idonsune, hakanne yasaka sarkin mota matso da motar bisa alfarmar ma'aikatan wajen, suna gama sakkowa k'afarta ta rik'e, dole ya d'auketa daga ita har nauyin cikin ya k'arasa da ita motar, mutane duk tausayinta yakamasu. Tunfa a mota labari yafara canjawa, dan Munaya tafita hayyacinta sosai, Galadima sai tsawa yakema sarkin mota, ALLAH daine kawai ya kaisu asibitin lafiya, aiko suna shiga dogarai suka shiga da gudu cikin asibitin kiran doctors. Tunima Galadima ya kuma sunkutarta yayi ciki, a hanya yagamu da nurses da gadon d'aukar marasa lafiya, bai d'orataba, yawucesu abinsa, doctor Farida ta nuna masa d'akin da aka canjama Munubiya. Gadon da aka tanada dan Munaya ya d'orata, Munubiya tashiga mik'o mata hannu tana kuka, itama a wahalce tamik'a mata nata, dan gadon kusa da kusa aka sakasu.... A tare suka dinga Neman yafiyar junansu suna kuka, sai tausayinsu ya kamasu Galadima. Da k'yar doctor Farida tasamu Galadima ya fita suyi aikinsu, dama haka tasha dagama da Yaa marwan shima, saida ma Abbansu yamasa magana, Dan shima yana asibitin. Munubiya da Munaya Haka suke rik'e hannun juna kowa nashan azabar nak'uda, (wannan k'auna dabance gaskiya, nak'uda ba abun wasaba amma suna son jin junansu a kusa, wato koma mutuwace tazo musu a tare?😽). Haihuwar Munubiya ce tafara gadan-gadan, Dan haka Munaya ta k'ank'ame hannun y'ar uwarta tana kuka da kiran sunanta a galabaice, itama sai labarin yafara canjawa, Nurse da doctor Farida and doctor Zainab dake Kansu duk suka maida hankali ga Munubiya, cikin rahamar ubangiji saiga jinjiri yayi sallama duniya da kuka. tamkar jira itama Munaya ta kar6a, a time d'in Munubiya tayi shid'ewar wucin gadi, amma hannunta na cikin na Munaya datake shan azaba itama. Ba'a d'auki tsawon lokaciba itama tata mace tafito, saikuma sabuwar nak'uda ta tashi a tare suduka, yanzu Munubiya mace Munaya kuma namiji, na Munaya na fad'owa wani yakuma biyo baya😳. Turk'ashi, ALLAH sarkin rahama da tausayi, maiyin yanda yaso kuma ga Wanda yaso, Munubiya ALLAH yabata k'autar tagwaye mace da namiji, yayinda Munaya keda uku, maza biyu mace d'aya. Su doctor Farida duk sun kacame da murna da k'ok'arin gyara yaran, kaikace su akama haihuwar. Dandanan aka shiga goge yara da zaitun, amma cikin hattarar kar a had'esu agaza ganewa.. Su Munaya ma dai kulawa ta musamman aka basu, amma Munubiya ta suma, kuma bata farfad'oba, hakanne ya tada hankalin su doctor Farida suka rufu akanta suna bata dukkan wani taimako, sama-sama Munaya ma kejin 'Yar uwarta tashid'a, hakanne yasata kuma k'ank'ame hannunta hawaye na zurara mata, itama bawani k'arfine da itaba, Dan ko idanu dak'yar take iya d'agawa, dishi-dishima take ganin komai. Lamarin yana san zama babba, Dan saida wani babban doctor ya shigo dole, ganin shigi da ficinsu doctor Farida yayi yawa yafara ankarar dasu Galadima. Nanfa suka fara turkesu da tambayar ko lafiya?, sukuma suna basu amsa da babu komai, kowa dai bai yardaba, dukda suna jiyo kukan jariran. An d'auki wasu adadin mintuna kafin numfashin Munubiya ya dawo, ajiyar zuciyar da Munaya tasaki duk saida yasaka su doctor Farida kallon ta da tausayi, dukda tana cikin wani hali itama, amma hankalinta nakan 'Yar uwarta. Sun kimtsasu tsaf, daganan aka musu allurar barci dansu sami Hutu, yara dai kam Alhmdllh, duk da sun lura d'aya daga cikin na Munaya bai cika kuzariba, kamar sauran mace da namijin sun fishi lafiya, amma basuda tabbas tunda basu bincikaba. Nurse d'aya tafito ta kar6i kayan haihuwar takoma, duk an saka musu, dukda basu zama iri d'aya ba tunda sunzo babu tabbacin miza'a haifa, musamman ma su Galadima, gara su Yaa Marwan sunsan ita Munubiya dama biyune. Tunda su doctor Farida suka fito Galadima dake ta kaikawo shida Yaa marwan da Muftahu suka maido hankalinsu Kansu, Galadima bai iya matsawa ba, saisu aunty mimine suka k'arasa ga su doctor Faridan. Kowa yana k'ok'arin tambayar abinda ke faruwa. Doctor Farida tayi murmushi, tace, “to ai bakine bazai iya fad'a ba ma, inaga kawai angunan k'arnin su shiga daga ciki, idan sun fito kwaji komai”. Yaa marwan da Galadima suka kalli juna, kowa yana fargabar abinda zai tarar d'in. Aunty Mimi ce takama hannayensu tana fad'in “kuje mana, mi kuke tsorone wai?”. Kowa tamkar an doke masa gwiwa haka suka nufi d'akin, Yaa marwan ne gaba Galadima a baya.. Duk sukayi sororo a k'ofar d'akin suna bin gadajen matan nasu da jariran kusa dasu da kallo. Badan kowa yasan kayan jikin matarsa ba dabasu iya banbancewa ba (kunsanfa mu 9ja 'yan gargajiyane🤭, kod'an canja kayannan na asibiti bamayi🤣). Galadima da Yaa marwan suka kuma kallon juna, kowa ya kasa cewa uffan, doctor Farida dake bayansu tamkar ta kwashe da dariya, tadai daure ta danne. Ra6asu tayi ta shigo ciki sosai, ta tsaya tsakkiyar gadajen tana kallon hannun Munaya da Munubiya dake had'e da juna har yanzu, sunyi-sunyi su saki amma sunk'i, sai suka saka musu lokar asibiti a tsakkiyar aka d'ira hannayen Dan kar suyi sanyi.. Juyowa tayi ta kallesu da murmushi a fuskarta, tace, “wannan itace Munubiya ga babies d'inta nan 2 mace da namiji, wannan kuma Munaya ga nata 3 maza biyu mace d'aya. Ina muku fatan alkairi gaba d'aya, ALLAH ya rayasu akan sunna”. tana gama fad'a ta juya ta fita tabarsu. Binta sukayi da kallo harta fice, sannan suka maido ga iyalan nasu, saikuma kowa ya k'arasa da hanzari ga matarsa. Yaa marwan yasaki murmushi yana d'aukar macen, sanan ya d'auki namijin shima, dukya rungume. Galadima kam durk'usawa yay gaban gadon yasa gwiywoyinsa a k'asa ko k'yank'yami bayayi, dukda angyara wajen tsaf tamkarma ba'a haihunba. Hannunsa d'aya ya d'ora agoshin Munaya da duk yaga ta masifar rame masa yau, d'ayan kuma yafara tsafa kumatun yaran d'ai-d'ai, hawaye masu d'umi Wanda shikad'ai yasan ma'anarsu suka fara sauka a kumatunsa. Cikin lumshe ido ya matsa ya sumbaci goshin Munaya da hancinta, sannan ya dawo kan babies nashi yana sumbatarsu. Yaa marwan ma yanacan ya duk'ufa kan matarsa yana mata kalamai masu dad'i acikin kunne k'asa-k'asa, kai kace idonta biyu tana jinsane😹. Galadima ya share hawayen fuskarsa, cikin murmushi yace, *“UBANGIJINA ka gamamin komai, yau nine da k'yautar abin cikin kwan d'ai-d'ai har 3 a lokaci d'aya, badan k'arfina kabaniba, bakuma Dan nafi sauran bayinka ka baniba, suma y'ay'a jarabawace ga iyaye, ya Mahaliccinmu kabamu ikon bama yarannan tarbiyar da zasu zama cikin alfaharin MANZON ka da addininmu mu da mahaifansu mata, ka rayasu bisa turbar addinin islama, ALLAH yasa suzama masu tausayi da jink'ai gana k'asa dasu damu kanmu, su zama masu girmamawa da mutunta na sama dasu a duk inda suka shiga, ya RABBI ka rinjayar da zukatansu ga bautarka domin rabauta a duniya da lahira, ka nisantar da zukatansu da gangangar jikinsu ga sa6onka komin k'ank'antarsa dagasu har 'yan uwansu gasunan guda biyu da k'annensu masu zuwa da dukkan y'ay'an Al'ummar musulmi. I love you so more and more my Darling children's, ina muku barka da isowa duniya gidan gwagwarmaya, ALLAH yabaku damar cinye jarabawar da ubangiji ya k'addaro a cikin tsawon rayuwar da zakuyi a dunia kafin Ku koma garesa”.* Yaa marwan ya amsa da amin shima fuskarsa d'auke da murmushi. Tashi Galadima yayi yaje gareshi suka rungume juna. Galadima yace, “d'an uwana ina tayaka murna”. Yaa marwan ma yace, “ranka ya dad'e nima ina tayaka murna”. Sakin juna sukayi suna dariya, saikuma suka kuma cafke hannun juna cikin musabaha da nuna tsantsar farincikin dake baibaye da zukatansu a yau d'innan. Aunty Mimi kasa hak'uri tayi ta danno kai d'akin babu ko sallama. To shigowarta cefa ta fallasa komai, kowa yasan d'unbin alkairin daya sauka a wannan families guda uku a yau. Dan danan labari yafara karad'e asibiti da gidajen su Galadima Dana su Munaya. Masarautar gagara badau, masarautar su papi, su Momma duk labari ya Isar musu harda hotunan babies gaba d'aya, kafin kacemi labari yafara zagaye social media, *FANS NA RAINA KAMA FA* babu ala, dama duk sungama shirinsu, (danma ansamu sa6ani masu tafiya india🤣, Wanda basu kai ga tafiya ba ALLAH ya taimakesu saiku tattala kud'in jiyginku babu ruwana😹😂🤸🏻‍♀). Bakin Galadima da Yaa marwan da dukkan ahalin wad'annan dangi kam yakasa rufuwa, hardamu ma masoyansu. Yauma dai su doctor Farida da jama'ar asibiti sunsha k'yaututtuka, Dan Muftahu ya baza abin mamaki, ( lokacin da su sarkin mota zasu fitone yagansu kamar a rikice, shikuma zai fita daga masarautar shine ya tambayesu, sarkin mota ya fad'a masa, bai bisuba saiya wuce asibiti, shine yasaka aka canjama Munubiya d'aki, aka tanadi gadon Munaya kuma). dukda Galadima yayi mamakin ganinsa hakan bai sakashi tambayarsa ba ko katse masa hanzari, ko'a fuskama bai nuna mamakiba. *************** Mama Fulani Na kishin gid'e bisa kilisarta kuyanginta Na bautar da suka saba, Wambai na gefenta yana nuna mata pictures na gidaje dayake son za6ar d'aya daza'a gina masa shima acikin masarautar, don mama Fulani tamatsa suyi aure, shi matawalle yamace bazai zauna da matarsa a k'asarba. Amma mama Fulani tace dolene saiya zauna. Wata baiwace ta shigo jikinta sai 6ari yake, ta zube a gabansu tana huttai, Wambai ya daka mata tsawa. Firgita tay tayi baya zata fad'i, Mama Fulani ta d'aga masa hannu alamun ya barta. “haba Granny kina ganinfa yanda ta shigoma mutane a haukace, saikace wasu sa'ointane a wajen?”. Uffan mama Fulani batace masaba, sai wani k'asaitaccen murmushi datayi tana kallon amintacciyar baiwarta, alamu tamata da ido na ta tambayi mi dattijuwar tazo dashi?.domin itace dama mai kawo ma mama Fulani duk wata gulma takowane 6angare a masarautar, Dan ita babu sashen dabata da 'yan lek'en asiri, kuma wannan dattijuwar baiwa itace shugabarsu, komai suka tattaro ita zasu fad'awa ita kuma takawo ga mama Fulani. “mike faruwa tulluwa?”. Amintacciyar baiwar mama Fulani ta fad'a tana kallon dattijuwa tulluwa dahar yanzu jikinta baibar 6ariba. “Ranki ya dad'e ki gafarceni da abinda nazo fad'a, banida za6in daya wuce hakan, domin da kiji a bakin wasu gara kifara ji abakina danki tabbatar nasan aikina”. Mama Fulani ta hura hanci, yayinda izzarta ta k'aru, sosai ta tashi zaune idonta akan tulluwa. Batareda tace uffanba tulluwa tacigaba da magana, Dan tasan ma'anar kallon ta cigaba da magana kenan. “ranki ya dad'e yanzunnan labarin haihuwar matar Galadima ta iso wannan masarauta, ba haihuwar baceba abin girgiza abinda ta haifanne, idan kinbani izini sai na fad'a uwar gijiyata”. Wani kakkauran yayu mama Fulani ta had'iye, Wambai daya cika yay fam da haushin wannan shegiyar baiwar ya Dalla mata harara, “dalla malama kifad'a kinwani zauna cancana magana kamar wata zuma”. “ALLAH ya huci zuciyarka ranka ya dad'e, maganarce tanada nauyi. dama labari ya iso ta haifi yara uku ne maza biyu mace d'aya....” Wambai yay masifar razana harda mik'ewa, mama Fulani kam ko motsi batayiba, sai wani k'ayataccen murmushi na k'asaitattun mata masu izza da mulki tayi, ta d'ago ido ta kalli Wambai cikin harara tace “kai kuma miye na mik'ewar?”. Tunawa yay akwai kuyangi saiya saki murmushi basarwa, yace “mamaki mana Granny, 'ya'ya uku fa a 1 time, dolene na taya d'an uwana murna ai”. bai jira cewarta ba yafice da hanzari. Lumshe idanu mama Fulani tayi bayan Wambai ya 6acema ganinta, ta kalli amintacciyar baiwarta fuska d'auke da murmushi nan tace araba k'yaututtuka, takuma sallami kowa. K'yaututtukan da mama Fulani tasaka a rabama bayin gidan yasaka zancen haihuwar munaya yakuma karad'e lungu da sak'o na masarautar, masu murna nayi masu kuka nayi, dan kowa dai yasan magadan masarautar gagara badau sun iso, tunda kowa yasan Galadima ne magaji mai jiran gado, _(karku manta haryanzu sarkin yanzu sarautarsa ta ruk'on kwaryace, Dan mahaifin Galadima tsohon Sarki bawai mutuwa yayiba, sannan ba murabus yayi da kansa yace yabarma Sarki na yanzu sarautarba, so sarautar ruk'on k'warya yakeyi, kuma ko a yanzu tsohon Sarki yasamu lafiya dolene ya sauka yabashi kujerarsa, mai guri yazo kenan, mai tabarma dolensa ya nad'e🤷🏻‍♀)_. ************** A 6angaren gidansu Munaya ma bata canja zaniba, Dan hassada k'ararace tafito a fuskokinsu da matuk'ar razanuwa, kenan arana d'aya Innarsu munaya ta wayi gari da jikoki 5 kenan? miyasa a komai sai Ai'sha ta fisu ne? bayan kuma sun fita gata sun fita dukiya, sukeda dangi da tarin 'ya'ya a gari, suke da ilimin zamani, k'asarsu ce ba karoro sukazoba?. Innaro kam dai tadage sai zuba gud'a take da taka rawa, gud'artace ma ta ankarar da jama'ar anguwar mi ake ciki, dandanan aka cika mata gida ana tayata murna. Babu kunya tasaka Shu'aibu ya kaita asibitin, bayan kwanakin munubiya biyu akan gwiwa kuma tasani amma bata ta6a nuna sha'awar zuwa dubata asibitin ba ma.😏 *************** Tunda kuyanginta suka fice tamik'e zaram itama, safa da marwa tafarayi na tsantsar tashin hankali a makeken falonta daya gama jin kayan alatu tamkar bana tsohuwa ba, zufa dukta jik'eta sharkaf, sai kuma maimaita fad'in “y'a'ya uku? Y'ay'a uku fa? wannan 'yar yarinyar ta haifa y'ay'a uku?, kai banma yardaba gaskiya, kodai k'aryane basuji d'ai-daibane?. jikinta na rawa ta jawo wayarta tayi Kiran Momma. Momma dake cikin tsantsar farinciki saboda isowar labarin haihuwar jikokinta sabbi fil a Leda har uku, ta d'aga kiran mama Fulani. A mutunce ta gaisheta kamar yanda ta saba koyaushe. Mama Fulani bata amsaba, sai tambaya data jehoma Momma, “Zeenah ashe matar d'anki ta haihu? Amma aka kasa sanarmin sai dai naji a jita-jita?”. Murmushi momma tayi, tace, “ranki ya dad'e a gafarceni, amma Nima yanzunnanma nakeji, dan suna isowa Nigeria tafara nak'uda tun a mota”. Cikeda mamaki mama Fulani tace, “yo a ina ta haihun?”. “anan Nigeria ne ai mama”. “Ai nazata anan India ne shiyyasa na kira, to ALLAH ya raya, bara nasa a bincikan asibitin”. bata jira cewar Momma ba ta yanke wayar, murmushi kawai Momma tayi tana girgiza kai, ta k'agara Abie ya tashi a barci ta guntsa masa wannan daddad'an labari. Saman kujera mama Fulani ta jefa wayarta tana cije la66anta da sakin wata k'aramar k'ara hawaye na zubo mata, ita kuma tata ta k'are, Matawalle ya dace da haihuwar wad'annan 'ya'yan ba Galadima ba, dolene tanemo mafita da gaggawa kafin lokaci ya k'ure mata. 🤣🤣🥴 ★★★★★★★★★★ Kiran Momma daya shigo a wayar Muftahu ya saka shi mik'ama Galadima, dama shiya kirata ya Sanar mata haihuwar, ganin haka ta kirashi danya had'ata da Galadima, tunda taga suna tare. Hakkanne yasaka Galadima fitowa harabar asibitin yana amsa mata, cikeda tsantsar farin ciki suka shiga taya juna murna, ya tambayi ina Abie, ta Sanar masa yana barcine. Momma tace, “an sallamekune?”. “a'a Momma, har yanzu suduka barcima suke, gashi magriba ma ta gabato anan, banama zaton sallamarnan yau, maybe sai zuwa safiya”. Ajiyar zuciya momma ta sauke, tace, “to Muh'd yau fa barci bai gankaba, dolene idonka yazama abud'e tundaga kan doctors, Nurse's, da makusantanka, hankalin duk wani idon mak'iyinka yanzu akan wad'annan bayin ALLAH guda uku yake, sunsan shine kawai tarko mafi tsauri dazasu maka a yanzu, su zaituna suna hanya itada kuyangi 5 amintatu da zasu zauna daku, itama Zaitun (mom) bazata komaba sai anyi suna, anayin suna kuma Munaya zata koma gidansu tayi wanka irin na al'ada da kowa ya Sani, tunda kasan dokar masarautar taku kenan. Wannan kawai shine mafita”. Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, muryarsa cike da damuwa yace, “insha ALLAH Momma duk za'ayi hakan, amma zama gidan nasu bak'ya ganinsa kamar had'ari? tunda za'a iya tsutar dasu a can, dan babu wani tsaro”. Murmushi Momma tayi har Galadima najin sautinsa, tace, “nasan abinda nakeyi ai Muh'd, bazance aturasu canba nasan zasu cutu, kaidai kawai kayi hakan, sauran bayani saika dawo zakaji komai, su zaitun nasan suna gab da isowa insha ALLAH. Papi ma yace yakira wayarka bata shigoba daga kai har Haneefa”. “tab, yoni Momma ai banmazo da waya ko d'aya ba wlhy, duk nan na mantasu a mota, kima saka khumar ya kawo miki, saidai zuwa Safiya nasamu k'arama na r'ik'e”. “to shikenan, dama haka nafad'a masa nima maybe kabar wayoyin anan, idan ta farka dai a kirani naji muryar d'iyata nima, konaji sanyi”. Murmushi Galadima yayi yace “insha ALLAH Momma”. Koda wayar ta yanke saiyayta juya maganganun momma a ransa yana musu fashin bak'i d'ai-d'ai. Haka ya koma zuwa cikin asibitin, dan anfara addabarsa da kallo, shi saiya rasama mi suke kallon? Shidai bayasha banban da sauran halitta bane, bakuma za'a kallesa ace ba bak'in fata bane, bakuma wasu kayan ado na musamman ya sakaba, hasalima k'yank'yamin kayan jikinsa yakeyi, dan sun kwana suna Neman yini a jikinsa, (tunda ba time d'inmu d'aya da India ba) yaja guntun tsaki yana k'arasawa ciki ya mik'ama Muftahu wayarsa. *********** Sai bayan isha'i su mom suka iso, dan basu sami jirgi da wuri ba, a lokacin jama'ar gidansu Munaya suna asibitin, masu kukan zuci nayi masu murna da gaskiya nayi, hakama a wasu daga masarauta suna nan, wasu lek'en asiri kawai aka turosu, wasu ko na taya farincikine da tabbatarwa. Yau dai yan gidansu Munaya suna kallon abin mamaki, da gaske dai inna Ai'sha tamusu fintinkau irinna jirgi, saidai hange daga nesa da harara cikin duhu. Mom bakinta yak'i rufuwa, harda rungume Galadima, Nuren kuwa hardasu taka rawa🤣, Muftahu na masa lik'i. Mutane abin ya birgesu, Galadima yay murmushi yana d'an dukan kafad'ar Nuren da Muftahu kawai. Su Munubiya basu farkaba har sannan, doctors sunce babu wata Matsala, a barsu su huta sosai yanda zasu tashi da kwarinsu zuwa Safiya. Dole dai Galadima yasa aka zuba police a asibitinan ranar, sauran kuma anbarma UBANGINJIN TALIKAI dake kallon motsin kowa. Masu tafiya duk suka tafi, aka bar masu kwana kawai. Galadima da ya dage anan zai kwana shima, da k'yar dai mom ta lalla6ashi ya tafi gida kodan yasamu yad'an huta, kallo d'aya zaka masa ka gane a matuk'ar gajiye yake, jijiyoyin Kansa sunyi rad'a-rad'a, ga yunwa waddama ya manta da ita da alama. Wannan dare dai ya kwana rayashi da bautar ALLAH ne da godiya mai yawan gaske. Innarsu Munaya ma dai kuka sosai tasha na dad'i, itama haka ta raya wannan dare, hakama Abba, shima yamik'a godiyarsa ga ALLAH dan lokacin dayake buri da tanadi ya cika, koba komai zai sauke nauyin dake rataye a wuyansa insha ALLAH. Washe gari...............🤩✍🏻 *_media ko bala'i, kayi turanci a novel ace ka cika iyayi da son asan ka iya turanci🤦🏻‍♀, muda muke koyo muyi ace bamusan abinda mukeba🤦🏻‍♀, kai jama'a babu mai iyama 'yan social media sai ALLAH, ko uwarka ka yanka kagasa tasha mai kwallan tana d'iga, da wani yagama ci zaice bataji gishiri ba🙄, ALLAH ya shiryar damu muda bakunanmu dai.🙏🏼._* _Ayshan sadiq sak'onki ya iso gareni, nakuma gode kwarai da gaske, saidai ina mai baki hak'uri da sauran fans d'ina, a gaskiya weekend d'inan ina muhimman abubuwane a cikinsa, bazan iya alk'awarin typing ba, sannan ni kaina idanuna 👁👁da Brain 🧠 d'ina suna buk'atar hutu, inada aure, akwai wasu hak'k'oki a kaina bana typing kawai ba, kunga yadace suma na basu lokacina, dan Ku gamsu nake zaman yin typing mai tsawo, insha ALLAH idan mukai hak'uri kamar yaune raina kama zaizo k'arshe abarma yayinsa Ku manta dashi saikuma wasu dazasu 6ullo daga sauran writers namu, dan haka muringa hak'uri da abinda ALLAH ya k'addara namu a lokacin da ya tsara, kar muyi gaggawa domin aikin shaid'ance, nima Ku duba nawa buk'atun amatsayina na mutum kuma mace mai rataye da igiyar auren. Ina godiya kwarai da gaske da k'aunar da kuke nunama wannan buk, bammasan yanda zan nuna muku farincikina ba kusan inajin dad'in Comments naku nima, amma ina sonku irin sosai d'inan a raina, kumuje zuwa guys, duk Nisan jifa k'asa zai fad'o👎🏻_ I love you mazga-mazga all.😘😘🥰🥰😍😍😍🤝🏻. Ayshan sadiq, ina miki fatan alkairi a duk Inda kike😘😘😘😅🤝🏻. *_ALLAH ka gafarma iyayenmu_*🙏🏼😭 [7/9, 11:05 AM] ❤y'ar K'asa❤: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣3⃣ ...............Koda Muftahu ya sauke Galadima saiya sake shiri Yakoma asibitin, tunda ya shigo idon Nuren a kansa, sai mamaki ya kamasa, shin miya maido Muftahu asibitin? bayan kuma tare suka tafi da Galadima. Bai masa maganaba dan karma yasan ya gansa, saiya saka ido a dukkan wani motsin Muftahu d'in, shidai Muftahu baisan yanayiba, dan baima je d'akinda su Munaya sukeba, sai zagaye-zagaye dayaketa famanyi har ALLAH ya wayi gari lafiya. Wannan lamarifa ya zaune a zuciyar Nuren yanata kaikawo, anya kuwa ba suna zargine akan abinda ba haka yakeba?, dukda jami'an tsaro dake wajen Muftahu Nada damar aiwatar dadukkan abinda yay k'uduri tunda kowa namasa kallon makusancin Galadima, amma har ALLAH ya wayi gari baimayi wani yunk'uri na shiga d'akinba balle alamun rashin gaskiya, saima aikinsa dayay kama dana mai k'ok'arin bama wani abu kariya, “ya ALLAH ka warware wannan lamari cikin sauk'i kodan wannan bawa naka yasamu nutsuwa shima”. Nuren ya fad'a a fili yana d'aga hannayensa sama alamar rok'o. Muftahu dake kallonsa yay murmushi yana amsawa da amin a la66ansa, daga nan yafice abinsa ya koma masarauta, saboda anata kiraye-kirayen sallar asubahi **************** Misalin 7:30am Munaya ta farka, kamar a kunnen Munubiya itama saita farka, su mom dake d'akin suka shiga musu sannu, cikin tsantsar farin cikin farkawar tasu, dandanan aka kira doctor. Alhmdllh babu wata matsala a tattare dasu, aka kikkimtsasu dagasu har yaran daketa barci irinna jinjirai, daga Munu... Har munaya dai kallon y'ay'a biyar sukeyi, amma tunaninsu ko cikin y'ay'an y'an uwansune. Doctor Farida data lura da hakan tayi murmushi kawai. umarni tabama Nurses d'in abama kowa nata, kallon kallo akeyi tsakanin Munaya da Munubiya, amma kowa bakinsa yagaza furta komi, saisu kalli juna sukuma kalli jariran gabansu. Doctor Farida dai dataga basuda niyyar d'aukar yaran tace “y'an biyu wannan itace k'yautar da ALLAH ya baku, Munubiya 2, Munaya 3. Duk waro ido sukayi, Dan Na Munaya ne yabasu mamaki, tunda dukansu sunsan Na Munubiya dama. Munubiya ta sakko daga gadonta batareda ta d'auki ko d'a d'aya anata ba, gadon Munaya ta nufo, ta durk'usa k'asa tana rungumo yaran, ga hawaye ga dariya tanayi, saikace sokuwa. Munaya ma dai batabi takan nata d'inba, saita nufi Na Munubiya ta d'auka duk ta sakasu a jikinta, k'aunarsu Na ratsa dukkan 6argonta kamar yanda take k'aunar mahaifiyarsu. Galadima da Yaa marwan dake tsaye a bakin k'ofa suka kalli juna suna murmushi, kowanne yana mamaki a ransa, anacewa y'an biyu akwai shak'uwa, sukam suna mamakin ta wad'annan Matan nasu, soyayyar dake tsakaninsu tanada ban mamaki da birgewa. Galadima ya k'arasa ga Munaya da har yanzu take a tsaye idonta arufe y'an biyun Munubiya na jikinta, had'ata yay itada yaran ya rungume. A firgice tabud'e ido, saitaji k'amshin turarensa, tayi baya kad'an yay saurin ruk'ota. Idonsa ya saka cikin nata yana wani murmushin dabata ta6a ganiba daga garesa. Ahankali ya furta haba “Maman y'an biyar a hankali mana”. K'aramar harara ta sakar masa, ya saka k'aramar dariyar da tadawo da Yaa marwan daga duniyar daya tafi😳, danshifa mutunmin naku har yana Neman sakin layi🤭🥳. Mom dake bayansu tayi gyaran murya, kowa saiyaja baya daga jikin matarsa🤣, suna wani susar k'eya. Munubiya da Munaya sai suka koma kusa da juna, Munaya ta kama hannun Munubiya a cikin nata. ita mom dariyama suka bata, Dan haka tad'an dara tana fad'in “An sallamemu to yanzu ya za'ayi?”. Munubiya da Munaya suka kalli juna, da alama dai basa buk'atar rabuwa, sudai su Galadima kallonsu suke kawai. Ganinfa zasuyi daru sai mom tai murmushi, da ido taima Galadima da Yaa marwan magana akan su fita. Babu musu suka fice, itakuma takama hannun Munaya da Munubiya ta zaunar a bakin gado. Magana take musu k'asa-k'asa wadda (banajin🙄). Sai naga duk sunyi murmushi suna 6oye fuska. Itama murmushin tayi tana saka musu albarka. Dan murmushin nasu ya tabbatar mata dasun amince. Daga nanfa shiri aka fara, kowacce aka had'a mata kayanta da y'ay'anta. Gayyar gidansu Munubiya su mama Rabi'a suka kwashi nasu, nasu Galadima ma haka. Manne da hannun juna suka fito, mutane sai kallonau sukeyi abin sha'awa da birgewa. Harda masu musu hotuna daga gefe.. Su doctor Farida ma saida suka matso akayi musu hoto danya zama acikin tarihin wannan asibiti. Saida Munubiya ta saka munaya a mota sannan takona tashiga wajen mijinta itama, kowanne Na share hawaye, ba'a San ransu za'a rabasuba. Saikace wad'anda za'a raba gaba d'aya🤣, kai ALLAH yabamu 'yan biyu😂⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. ★★★★★★★★★★★★ Tarba ta musamman su Munaya suka samu a masarauta, harma abin yaso basu mamaki, hakan dai baisa Mom tayi sake da yaran ba, duk wani motsi dai idonta Na Kansu, an musu rakkiya har sashensu dayasha gyara, yayinda Galadima keta kar6ar barka ga ahalin wannan masarauta, tun daga hadimai zuwa y'an uwansa na jini, maza da mata yaro da babba. Za'ayi walimar cin abinda data sannu da zuwa ga y'an uku a masarautar k'arfe 8pm, wannan yasa ba'a jimaba aka barsu suka shige Dan Munaya tasamu ta huta. Mamaki ya kama Munaya ganin an cika mata gado da tarkacen Teddy's, wannan abun haushi da yawa yake, kuzo Ku kama jera d'iyan aljanu agado kawai. Sudai su mom suka jasu gefe aka kwantar da yaran, itama zama tayi abakin gadon tana dafe kai. Aunty Mimi tace, “lafiya dai k'anwa?”. “wlhy kaina ke ciwo aunty mimi”. Sannu suka shiga yimata, mom tace, “bara laraba tazo ayi wanka kisamu kici abinci saiki sha magani”.. Munaya ta amsa da “to” tana d'an kwanciya a bakin gadon. ********* Laraba amintacciyar baiwar inno tama Munaya cikakken wanka da babu algus acikinsa, itako sai raki takeyi da zille-zille. a haka dai aka gama wannan wanka, lokacin da suka fito sun iske yaranma Mom tamusu da kanta, ana tsaka da shafesu da mai itada Aunty Mimi. Munaya dake d'aure da zani ta rufo babban towel a jikinta ta zauna a bakin gadon tana jingina da fuskar gadon, k'asa-k'asa take kallon yaran da mamakin anya kuwa itace wai ta haifesu? koda yake ba'a jayayya da ikon ALLAH ai, tanajin k'aunar yaranta a har cikin jininta, hakama Na y'ar uwarta, amma data tuna zasu rabu kwana kusa sai hawaye suka cika mata ido. A dai-dai wannan time d'inne Galadima yay sallama, hannunsa d'auke da Leda fara. Aunty mimi da mom dake sakama yaran kayan sanyi suka d'ago duk suka kallesa suna amsa masa sallamar. Idonsa akan Munaya datai masa kallo d'aya ta d'auke ido, murmushi yayi kawai ya zauna a bakin gadon yanama su mom sannu. Cikin tsokana mom tace, “aikin kud'i nikam nakeyi, musamman akan kishiya sa haushi, bar saurin godemin”, tai maganar tana dungure d'an hancin macen dake hannunta. Murmushi kawai Galadima yayi, sai Aunty Mimi CE ke bama mom amsa da “habawa Mom, dukfa kishinki keda Momma kwayi Ku gama, itafa wannan sarauniyar saita za6a ta darje ehe”. Mom tai dariya tana mik'ama Galadima ita, “yo da wannan nanannen hancinne zata za6a ta darje d'in? maji magani dai ai”. Galadima ya lumshe ido yana manna yarinyar da k'irjinsa, k'aunarta Na rsatsashi, ya sumbaci goshinta sannan ya bud'e idonsa, kwantar da ita yayi akan cinyarsa ya bud'e ledar yana fiddo dabino mai k'yau da tsafta, a bakinsa ya saka ya tauna, kafin ya d'ora bakin nasa akan na yarinyar ya zuba mata, da farko yamutse fuska ta shigayi, taji bak'on abu a bakinta, saikuma a hankali tafara motsa d'an bakin, galadima dai yana kallonta da murmushi, dadai taji zak'i saita mamule abinta. Mom tace, “oh su madan kamila kenan, anji zak'i”. Dariya duk sukayi, ya d'auketa yamata kiran sallar hud'uba a kunnenta sanan ya ajiyeta a gefe yana fad'in “ALLAH ya rayaki akan sunnah da tafarkin gaskiya”. Su mom suka amsa masa da amin. Kallon Munaya daketa shafa manta kamarma batasan dasu a d'akinba yayi, yanda taketa wani basarwa shi mamaki tabashi, baiyi zaton hakanba gaskiya, cayake zata nuna tsantsar farincikinta akan yaran?. janye idanunsa yayi ya kar6i d'ayan yaron. Shima haka ya tauna dabino ya bashi, sannan yamasa hud'uba da addu'a ya kwantar dashi. Kar6ar d'ayan ma yayi, Wanda bai cika kuzariba, yad'an masa kallon wasu mintuna yana tatta6a jikin yaron, sai kuma ya kalli mom da Aunty Mimi da suma kallonsa sukeyi. Mom tace “Yaya dai Sameer?”.. K'aramar ajiyar zuciya yayi yana shafa sumar yaron, “mom yaronnan kamar baida kuzarin sauran 'yan uwansa”. “nima na lura da gakan Sameer, amma maybe yanayinsa kenan, kasan kowa da yanayin da ALLAH yake yinsa ai”. “hakane”. ya fad'a cikin sauke ajiyar zuciya, sannan ya d'auki dabino shima yamasa tamkar sauran y'an uwansa, yaron yadad'e bai shanye dabinon ba, daga Bayama saiya fara kuka mara sauti. Rungumesa Galadima yayi yana hura masa k'aramar iska a kunne da d'an jijigashi, sai kuwa yayi shiru, shima hud'uba yamasa, ya kwantar dashi kusada y'an uwansa amma sai yaron yakuma Sanya kuka, gashi muryarsa bata fita da k'yau. d'aukarsa ya kumayi yana murmushi da fad'in “oh little Sameer what happen?”. Mom tace, “shagwa6a ce mana”. Dariya Aunty Mimi tayi, yayinda Galadima da Munaya suka murmusa, Dan duk abinda ke faruwa tana allonsu ta gefen ido, amma ta basar kamar bata d'akin. Fita Aunty Mimi da Mom sukayi suka barmusu d'akin. tuni 6angaren ya rikice da k'amshin girki, dan cikin kuyangin da su mom sukazo dasune suke tsara girki wa maijego dasu kansu. Tashi Galadima yayi d'auke da yaron a jikinsa ya nufi inda Munaya take zaune, tun d'azun tagama shafa man amma tak'i tashi ta saka kaya. Zama yay kusada ita sosai jikinsa har yana gogar nata. Da sauri ta yunk'ura zata mik'e, ya saka hannu d'aya ya ruk'ota yana maidata. Kallonsa tayi fuska a cunkushe kamar zata fasa kuka, idanunsa ya saka acikin nata yanda bazata iya janyewa ba, aiko duk k'ok'arinta nason ta janye d'in ta kasa, sai cika sukayi da kwalla, dan yana ganin k'yallin ruwan hawayen. Yad'an murmusa yana lumshe ido da bud'ewa a kanta. muryarsa cikeda k'asaita da sanyi yace, “kekuma salon taki murnar kenan?”. Had'iye kukan dake Neman kufce mata Wanda itama batasan dalilinsa ba tayi, tayi murmushin takaici tana janye idanunta daga cikin nasa, muryarta a sark'e cikin sanyin rauni tace, “Ina tayaka murnar sosai yalla6ai”. Lips nashi yad'an cije, ya lalla6a ya ajiye yaron da barci ya d'auka gefen y'an uwansa, Munaya duk tana kallonsa. Kuma matsawa yay jikinta sosai ya jawota jikinsa, batayi yunk'urin hanashiba, kamar yanda bata hana hawayenta zubaba. Ya saka tattausan hannunsa yana share mata hawayen, “Friend dukda bansan miya sakaki kukaba ina mai baki hak'uri, wannan ranar bana buk'atar damuwar kowa sai farinciki, musamman ma daga gareki, ina rok'onki alfarmar fansar wannan damuwar taki da farinciki akan kowanne farashi, komai tsadarsa kuwa”. ya k'are maganar da sumbatar sumar kanta. Murmushi tayi, ta d'ago daga jikinsa idonta akan yaran dake jere reras abin sha'awa. Shima d'in su yake kallo. “bana cikin kowacce damuwa da kake tunani yalla6ai, kawai dai...” sai tayi shiru. Kallonsa ya maido gareta, yace, “kawai dai mi yalla6iya?”. ‘ya k'are maganar cike da tsokana’. Ta murmusa tana mik'ewa tsaye, wardrobe ta nufa ta fiddo sabbin kayanta cikin na lefe, bata kuma kallonsa ba ta wuce bathroom domin saka kayan. Binta yay da kallo harta shige, yasaki miskilin murmushi yana kwantawa kusada yaran, a fili ya furta “yarinya nasan matsalarki”. yay maganar yana sumbatar kuncin na kusa da shi, sauran kuma ya shafa Kansu. A haka Munaya ta fito ta iskeshi, ya ta6a wannan ya ta6a wancan, kallo d'aya tamasu ta d'auke kanta. Sallamar da akayi a bakin k'ofar ya saka Munaya amsawa da bada izinin shigowa. Laraba tashigo d'auke da tire babba. Da sauri Munaya ta nufeta ta kar6a, Dan dattijuwace sosai, sannu ta mata tana fad'in “iya aida wanine ya kawo”. 'Yar dariya laraba tayi, tace, “dole na kula da amanar uwar gijiyata ai ranki ya dad'e”. Munaya da Galadima suka kalli juna suna murmushi, Dan sunsan inno take nufi. Laraba ta juya zata Fifa saboda ganin Galadima na nan. Kiranta yay ta juyo, yace, “zokiyi aikinki kar Inno taga ta rame tace baki rik'e amanaba, nima yarana abincinsu suke buk'ata”. Hararsa Munaya tayi, yay Biris kamar bai gantaba, saima d'an yatsansa daya saka cikin hannun yaron, shiko ya rik'e gam tamkar yasan minene. Laraba tace Munaya ta zauna ga abinci taci.. Yamutsa fuska Munaya tayi, kamar zatayi kuka tace, “wlhy iya bakina banajin d'and'anon koda yawuna ma”. “hakane ai saidai hak'uri ranki ya dad'e, dama wasu idan sun haihu sukanyi k'am baki, amma a hankali zai canja”. Badan munaya tasoba ta zauna, laraba tabata kunu mai k'yau da aka dama don ita, sai k'amshin kayan yaji yakeyi, sai farfesu. Kallon abincin kawai Munaya keyi, amma ko kad'an batajin sha'awar ci, ta tuna kwanakin baya da idan taga abinci jikinta har rawa yakeyi wajen son ci, hikimar ubangiji daban ce, ta d'ago ido suka kalli juna itada Galadima dake kallonta tun d'azu, a zuciyarsa yana tuna kwanaki uku rak dasuka shige, yanda ta maida abinci, murmushi yamata ta d'auke idonta ta maida ga abincin. A haka Mom ta shigo ta iskesu, zama tayi tana fad'in “yanaga bakici komaiba?”. Idon Munaya cike da kwalla tace, “ALLAH mom banajin d'and'ano”. Zama mom tai kusada ita, tace laraba taje itama ta karya. Kunun ta d'auka ta tsiyaya a Kofi ta d'iba mata farfesun, “kar6a maza runtse ido ki shanye kunun nan d'iyata”. Kunyar Mom ta sakata k'ar6a tana had'iye kwallarta, tafara sha badan tanajin dad'inba, sai dan tsatstsareta da ido da Galadima yayi shida Mom. ahaka dai tasamu tasha yafi rabi, dama yunwar takeji, dad'in bakinne kawai bataji, shima farfesun tad'anci, dandanan tafara zufa. tace, “Mom dan ALLAH bara na kunna AC”. “a ina?”. ‘galadima ya fad'a yana tashi zaune da sauri’. Ita mom ma dariya ya bata, yawani had'e fuska yana harar Munaya, “malama babu wani AC da zaki sakama mutane anan, kina ganin yara duk da mura sukazo duniya saboda rashin jin maganarki.....” Mom ta katseshi da fad'in “ai bama zai yuwuba, itada ke jego ko fankace a d'akinnan ai saidai kallo kuma, yanzu ruwan sha ma sai mai zafi”. Galadima ya sakko daga gadon yana fad'in “hakan ai shine dai-dai wlhy, remote d'in AC d'in ya d'auka a lokan gefen gadon ya masa yanda bazata iya control d'insa bama gaba d'aya, sannan yafice abinsa yana murmushin mugunta. Mom ta girgiza kai kawai, a ranta tana mamaki canjawar Sameer...... Maganarsa ce ta katse mata tunani, harya fita ya dawo baya, “mom ga maganinta nan tasha, kuma yaranan yunwa sukeji”. ‘yak'are maganar cikin marairaicewa’. Dakuwa mom tamasa, “Sameer kaci kidanku, wai yaushe kama fetsare hakane ban saniba?”. Fita yayi yana dariya, ta kirashi da sauri. Kuma dawowa yayi, tace, “kasandai Doctor tace a nemi madara, naga kuma bama kada niyyar hakan”. Gaba d'aya fara'ar fuskarsa ta d'auke, yad'an shafi girarsa da d'anyatsa d'aya yana fad'in “Mom wai wace madara ga abincinsu?, ALLAH dai ai shiya haliccesu, kuma shine zai wadatasu da abincin nasu, amma kawai sai a kama wani danna musu wata madara? dan ALLAH mu ajiye zancen madarar nan ma gefe mom”. Numfashi mom ta sauke, tasan murd'ad'd'en halin Galadima da dagewa akan ra'ayinsa, cikin kwantar da murya tace, “na yarda da maganarka, amma ita za'a tausaya mawa, shayar da yara uku bafa abune mai sauk'iba Sameer, wasuma d'ayane idan suna da fargabar shayarwa kaga duksun k'are sun lalace, koda dai sau d'ayane sai a ringa basu madarar a rana, tunda ALLAH dai baya hanaka yanda zakayi bane”. Tashi Munaya tayi tana hawaye, taje ta hau gadon kawai tayi kwanciyarta, ta kula Galadima yacika son kansa, tanaga saita tuna masa da matsayin auren nasu da alfarmar yarda ta haifa masa y'ay'an dayake neman nuna mata mulki a kansu, aidai abin shayarwar a jikinta yake, sai kuma yanda taso tayi da kayanta, dolene ta takama wannan homar tasa birki. Daga Mom har Galadima da kallo suka bita, yaja guntun tsaki yana juyawa zai fita. Mom tace, “zaka siyo d'in?”. A k'ufule yace, “zan duba”. Yay ficewarsa. shifa ya lura yarinyarnan ma batason yarannan, shin bak'in ciki take ALLAH yamasa k'yautar abinda kud'i baya sayane ko me? ALLAH zaiyi maganinta kuwa. 🤣🤣ho Galadima, uwa ta ta6a k'in d'antane🤦🏻‍♀. ★★★★★★★★★★★★ Mama Fulani dai yau tagaza gane kanta, duk yanda taso danne zuciyarta tayi murnar koda ganin idone ta kasa, shiyyasa ko zuwa wajen tarbarsu batayiba. Takuma hana dukkanin bayinta da kuyangi shiga inda take. Abinda bata saniba idon Galadima fes yake akan dukkan Wanda ya tayashi murna da samun k'yautar ALLAH, wad'anda bama su fitoba sun shiga black lists, kuma d'aya bayan d'aya saiya kartama kowa rashin m acikinsu. ★★★★★★★★★ Innaro kuwa dai saita hau tsiya dataji labarin su Munaya kowa mijinta ya d'auketa zuwa gidanta, tahau zazzaga masifa anmata ba daidaiba, babu Wanda ya kulata, dan masu zugatan suma hassada ta ishesu, basuda kuzarin taya 6era 6ari😂.. Haka tagama jarabarta takoma gida tana huci, Abba yasha dariya, danshi lamarin mahaifiyar tasu yanzu kallon rikicin tsufa kawai yake masa, inba rikicin tsufaba miye abin tada jijiyar wuya anan? Sunada damar hana yaran komawa gidajen mazajen sune?. Shikam baba k'arami ma lokacin da take jarabar zuwa yay ya ra6a ta gefenta ya fice daga gidan. Ai lamarin innaro sai ita🤣🤦🏻‍♀. ****************** A 6angaren Munubiya ma Alhmdllh, dukkan wata kulawa mama rabi'a tana tsaye akan 'yarta da jikokinta, sai zuba mata gata akeyi da k'yak'yk'yawar kulawa mai ban sha'awa. Suruka ta gari dadi alkur'an💃🏻💃🏻😘😘. ★★★★★★★★★★★★ Mom dai da k'yar suka lalla6a Munaya itada Aunty Mimi ta amince ta shayar da yaran, suna sha tana kukan zafi kuma😹, sunsan zataji zafi tunda Na farkone, ga yaran a buk'ace suke dama, amma kukan datake yawuce Na zafi kad'ai, (basusan harda haushi Galadima bane😂🤭). Mom data fahimci hakan saita fara lallashin da nuna mata muhimmanci hak'uri, su maza komai zasu iyayi akan y'ay'ansu, musamman ma shi da yake tsaka da d'okinsu yanzu, karma tabari irin wad'annam abubuwan su dameta, shima yafad'ane kawai amma zai sayo madaran”. Itadai Munaya kai kawai take d'agawa amma batace uffanba, dan tagama Sanin Galadima da halinsa Na kafiyar tsiya da dagiya akan ra'ayinsa. Bayan duk sunsha sun k'oshi Aunty Mimi tace ta kwanta ta huta kafin time d'in walimar yayi. ALLAH ya taimaketa maganin yasata barci kuwa, yaran Na gefenta suma suna nasu barcin, kowa cikinsa ya cika kenan😘. Ajiyar zuciya Aunty Mimi ta sauke tana murmushi, tace, “Mom d'an nan naki bazai canja ba dai ashe? lamarin Sameer saishi wlhy, koda bayaso susha madarar saiya fad'a da harshe mai dad'i ba fad'aba”. “Humm, kibari kawai, nifa harna fara murnar ya canja, Ashe yana nan yanda nasan kayana, yarinyar tanada hak'uri kuma wlhy, dan zama da mai halin Sameer saika daure, muma iyayen idan mun k'ureshi ba iya mana kawaici yakeba”. Aunty Mimi tayi dariya, “papi ne mai tankwarashi kobai soba ai, idan yak'i bari abasu madaran dashi kawai za'a had'ashi, komin wadatar nono shayar da yara uku ba sauk'i ne dashiba, balle ita farin Shiga ma”.. Mom tace, “hakanma shine kawai mafita ai”. *************************** *_8:15pm_* Liyafar cin abinci tafara gudana a babban d'akin taro Na masarautar gagara badau, Munaya da y'an uku duk sunsha k'yau, hakama uban gayya Baban y'an uku Galadima, duk d'insu sunci kwalliyane cikin ainahin kayan sarauta, yaranma an nad'esu cikin k'ananun alk'yabbu. (Gado kenan🥰) Kwai da kwarkwata Na gidan nan zaka sameshi a wajen, saidai marasa lafiya da wad'anda basa nan, mai martaba ma yana wajen, dan shine da Kansa ya shirya liyafar domin taya d'ansa murnar k'aruwa da kar6ar bak'uncin jarirai, yaran duk suna kusa dashi cikin d'an gadon da aka ajiyesu a ciki. Kowa anan yake zuwa ya lek'asu, yamusu addu'a. Yara sunsha addu'oi da k'yaututtuka ga iyaye da kakanni, abin zakkyau da birgewa. Ita kanta Munaya tasha nata k'yautar. ( k'yauta da bajinta kan saka zama isashe a gidan sarauta, wannan babbar al'adace tamasu mulki a masarautun k'asar hausa, shiyyasa suke ado da ita akowanne motsinsu🤩👍🏻). Tsakanin Munaya da Galadima babu uhum babu um-um, sai y'ar wullama juna harara (🤣nifa dariya suke ban), banga abin jin haushin junaba, duk da Na lura ita dama Munaya akwai haushi kaine ka jamin shan wahala😂, kaikuma Galadima k'asaita da jinkai ya sa kakasa fahimta balle kayi lallashi da kwantar dakai aji da y'an jariranka🤣. To maji dai maga yanda za'a kwashe😹. Sai 11 dai-dai taro ya tashi lafiya kowa ya kama gabansa. Shirin kwanciya Munaya tayi, suma yaran aka musu, saiga Galadima ya shigo cikin tasa shirin kwanciyar shima, mom tace, “yauwa Sameer ya za'ayi kwanciyar kenan? A falo zaka kwanta saboda tsaro ko?”. Murmushi Galadima yayi yana shafa kansa, yace, “kai Mom wai saboda tsaro”. “ALLAH kuwa Sameer, lamarinne yanada ban tsoro ai, dukda nasan ga dogarainan suma suna aikinsu, gakuma mu kammu, amma dole saida namiji a kusa, da canai shima Nuren ya dawo nan Ku had'u”. “mom kincika tsoro gaskiya, karki damu, ko ina Na sashennan akwai CCTV camera, kuma koyaya aka ta6a k'ofa ko windows akwai securitys a jiki zanji insha ALLAH”. “To shikenan Alhmdllh, ALLAH yak'ara tsaremu da tsarewarsa”. Galadima ya amsa da “amin” yana matsawa jikin gadon wajen yaran. Munaya dake saurarensu a ranta tace to ALLAH ya k'yauta, a gidanka kana zama saida tsaro inaga kafita?, amma jibarsu a awajen walimarnan kaikace kowa zuciyarsa fes take babu wani k'udiri, lamarin sarauta sai ALLAH, kaita buri tamkar ALLAH yamaka alk'awarin dawwama a cikin duniyar ne, bazaka mutuba bazaka tsufa ba, ALLAH ka iya mana da iyawarka, da ace inada dama saina cirema yaranan burin sarauta a ransu, amma ya zanyi, tarigada ta zama jininsu sai dai addu'a kawai....... Saukar numfashin dataji a gefen wuyanta ya sakata saurin dawowa daga tunanin data tafi, ta waigo da sauri sai taga Galadima. Fuska ta had'e shima yaci serious yana gyara zama. Waige-waige ta fara saitaga babu kowa a d'akin, ashe Mom ta fita. Baki ya ta6e ya nuna mata k'ofar bayi da d'an yatsa alamar mom tana ciki kenan. Cikin zaro ido ta kalli yanda yazo yawani shige mata, saitaja baya, ai da kunya dai mom ta fito ta gansu a haka wlhy. Yanda tayi d'in sai yaso bashi dariya, amma saiya had'iye, ya ciji lips nashi yana kallon yaransa, “tunanin mikikeyi ne? kinsan dai doctor tace jininki har yanzu bai gama sauka ba gaba d'aya, so ki kula, shi tunani baya kawo mafita sai matsala”. ya k'are maganar yana mik'ewa tsaye, itadai kallonsa kawai takeyi, bata ankaraba taji saukar tagwayen kisses a goshinta da kan bakinta. Idanu ta ware waje baki bud'e, ko kallonta bai sakeyiba ya fice abinsa yana murmushi. Mom data fito daga bayin ta girgiza kai kawai, don ganinda Galadima yamatane ya sakashi ficewa. Kallon Munaya tayi tace, “to rufe bakin kema”. Kunya ta kama Munaya taja bargo tarufe har fuskarta tana fad'in ka kasheni wlhy yalla6ai. A falonsa ya iske Nuren haryayi shirin barci shima, yana zaune yana shan tea da laptop a gabansa yana aiki, Galadima ya zauna yana sauke numfashi.............✍🏻 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏼_*l *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣4⃣ .............Kallonsa Nuren yayi da y'ar dariya, “angon jego ai dole kake sauke numfashi, irin wannan aiki dakayi haka? Y'ay'a uku fa a lokaci d'aya, a fuska dai kamar bazaka iya komaib.....” Nuren bai samu k'arasawa ba saboda filon kujera d'aya daki bakinsa, wanda Galadima ya jefa masa. Dafe baki Nuren yayi yana kallonsa cikin 6ata fuska. Galadima ya cije lips yana fad'in “cigaba mana parrot ”. Nuren ya cire hannun yana kwafa da jinjina kai, alamar zan kamaka ne. Galadima ya ta6e baki yana hararsa, “yaro aini yanzu na daina halin yara, sai dai kayi da wani kuma”. Dariya Nuren ya kwashe da shi, “o manya o manya, ai yakamata ma mai martaba yay murabus yabaka kujera kawai, kainefa Wanda kafara kafa tarihi a masarautar nan, Sarki Salisu barde shi yak'in filin daga yaje ya samo sunan gagara badau, kaikuwa yak'in kashe arna kaje kasamo sarakunan gagara badau”. Girgiza kai kawai Galadima yayi yana fad'in “kai dai d'an iskane wlhy, yakamata papi sumaka aure kodan y'ay'an mutane su samu lafiya ma”. “ni wlhy dama zakaje kace amin auren daka taimakeni”. Nuren ya fad'a cikin ta6e baki da d'aga kafad'a. Murmushi Galadima yayi yana gyara zama, “ALLAH ya shiryeka to, mike tafiya akan al'amura?”. Zama Nuren ya gyara yana komawa serious, “wlhy d'an uwa abubuwannan sun cika tsauri da yawa, a duka mutanen nan uku da yarinyarnan ta fad'a da gaske fa babu SD, amma ga pictures d'in wajen mutum 30 ka nunama Mumcyn Triple's ko zata ganeshi a cikinsu. dukansu yaransu tanderu ne, Sannan nifa inaga lokaci yayi da zaka binciki Muftahu face to face, dan lamarinsa yafara birkitan tunani gaskiya”. “kafad'i gaskiya Nuren, nima kuma ina tunanin hakan shine mafita, dan ni kaina lamarin nasa yafara kaini ga dogon nazari”. “To ALLAH yasa muji alkairi”. “amin dai”. Galadima yafad'a yana mik'ewa, “nifa na shige zan kwanta, ka kwana lafiya”. “ok ALLAH ya tashemu lafiya gwauro”. Galadima yay dariya, batareda ya juyoba yace, “duk lalacewar goma dai tafi biyar albarka tuzuru”. Nuren ya kwashe da dariya, yana fad'in, “oho dai, muma mun kusa zama gomar”. ★★★★★★★★★★★★ Zumid'i ya hana Momma komai, ta k'agara Abie yafarka yasha kanu, hakama su Samha su dawo school suji babban labari. Ana cikin haka saiga Sauban tamkar an jehoshi, babu kunya ya rungume Momma yana fad'in “wayyo dad'i Momma y'ay'a uku fa wlhy, kuma dai-dai da ranar haihuwar Yaa Sam, dan yau birthday d'insa wlhy, ciwon aunty gimbiya ya mantar dashi”. Itama rungumeshi tayi cikeda farin ciki, “hakane wlhy my love, yau ina cikin farinci mai tarin yawa, tarihi ya maimaita kansa da wani sabon salo mai banmamaki”. “Wlhy nima haka Momma, kallafa pictures d'in babies d'inmu”. Dukda tagani itama bata katse masa hanzariba ta kar6a wayarsa tana kuma kallo, harda na Munubiya. Momma tace, “kai yau innarsu yazataji, jikoki 5 a lokaci d'aya, baiwar ALLAH, dama mahak'urci mawadacine, tayi kukan shekaru masu yawa ga lokacin dariya kuma yayi”. “wlhy kuwa momma, nakira Yaa Sam batajeba”. “Ai yama manta wayoyinsa a nan, kasan sun tafi hankalinsa ba kwance ba, nima da wayar Muftahu mukayi wayar”. “wayyo Momma dan ALLAH kicema Yaa Sam mutafi gobe, wlhy kamar nayi tsuntsuwa na ganni a 9ja nakeji”. Dariya Momma tayi, tarasa inda zata saka kanta dan dad'i. Motsin da Abie ya farane yasakasu maida hankali garesa, idonsa ya bud'e ahankali a kansu. ganinsu tsaye kansa sunata murmushi saiya ma Momma alama da ido wai miya faru?. Da sauri Sauban ya rungumesa yana fad'in “Albishirinka Abie d'inmu, matar Yaa Sam y'ay'a uku ta haifa”. Ba k'aramin shock bane ya kama Abie, ya kalli momma alamar da gaske?. Kanta ta jinjina masa tana murmushi. Wasu hawayen dad'ine suka gangaro a kumatunsa, fuskarsa d'auke da k'ayataccen murmushi, A hankali yaketa jero Alhmdllh. Yace, “Mafarkina na shekaru da yawa yazama gaskiya Zeenah, tabbas ubangiji shine masanin gaibu, ya ALLAH na gode maka, godiya marar yankewa balle gajiyawa”. A hankali yake maganar Amma su Momma naji saboda sun matsar da kunuwansu. Dad'i duk yakuma lullu6esu, Abie yakuma fad'in “Zeenah wannan yarinya ta zama alkairi ga Ahalinmu, ALLAH ya albarkaci rayuwarta da abinda ta Haifa daku ma gaba d'aya”. Sauban da Momma suka amsa da amin. Yace a kira masa Galadima. A time d'in sunta neman Number Mom amma bata wuceba saboda Network, hakama ta Nuren da Muftahu, daga k'arshe dai sun hak'ura ne sai wani lokacin a sake gwadawa. Yau dai kam har doctor's d'in Abie sun shaida yana cikin farinciki, dan jikinsa ma ya nuna haka, k'arfin muryarsa ya k'aru, hakama bugun zuciyarsa dawasu yankunan halittun jiki dake bama d'an adam garkuwa, sun tabbatar a kowanne lokaci ALLAH zai iya gwada ikonsa ga wannan bawa, bayan tsawon shekaru daya d'auka a kwance sai an juyashi. Wannan albishir ya k'ara yalwata farin cikin wannan ahali, saima dasu Samha suka iso, duk sun rikice da ihun murna, yau d'in ta dabance a ransu. Isowarsu ce ta tunama Galadima da ranar haihuwarsa dai-dai da haihuwar yaransa, kuma dai-dai da haihuwar su Munaya ma😳😜. Wannan abin al'ajab da yawa yake, ita kanta munaya sai lokacin ta tuna, wayar Ayusher ta kar6a ta kira Munubiya tana mata tuni da ranar haihuwarsu. dad'i ya kama Munubiya ma, dan itama ta shafa'a, sai murna kan murna ta k'aru🤸🏻‍♀. ************************** Uban gayya dai Galadima da k'yar barci 6arawo yake sace sa a kowace rana, daya rimtse ido 'y'ay'an sa kawai yake hangowa, badan kar aga rashin hak'urinsa ba shikam da dasu zai ringa kwana. O baban zumud'i😘😘😽. A 6angaren yalla6iya ma hakane takan kasance, da taga laraba tayi barci dash Ayusher da Samha, (dayake itace take kwana dasu) saita tashi ta dinga d'aukarsu d'ai-d'ai tana runguma da musu addu'oi, jitake kamar ta had'iye kayanta ta huta kawai, takan dad'e tana Abu d'aya kafin barci yaci k'arfinta take kwantawa. Tosu yalla6iya anaso ana kaiwa kasuwa😂😜. ************************* Fad'a muku yanda abubuwa suka cigaba da kasance ga y'an barka ai 6ata lokacine ma, dangin Munaya ma sun taka rawar gani, Ayusher ma dai ta dawo nan zata zauna har ayi suna, hakama madam Innaro Galadima da kansa yaje ya kwasota🤣😜, aiko baki har kunne. Gaskiya fans sannunku da k'ok'ari, irin wannan tururwa haka, lallai kunma Galadima halacci shida yalla6iya, ALLAH ya saka muku da alkairi dai my sweetness🥰🥰🥰😘😘😘😘❤🤝🏻. Dole Galadima ya nemi waya da sim card ya lalubo su Abie da Momma d'insa da jakadiya dabasu samu zuwaba, suna shan hira a kullum shida su Abie ta video call, ga jarirai aita jera musu sunata shan kallo abin birgewa, Abie jiyake kamar yay tsuntsuwa ya gansa a 9ja, tsakanin nan yana cike da kewar k'asarsa ta haihuwa, yana fatan yakuma takata ko sau d'ayane kafin yabar duniya. “Insha ALLAH zaka taka da yawa Abie😭”. Mu tafi ran suna kawai😨⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Abubuwa da yawa sun faru a kwanakin bakwai d'innan, sai dai Alhmdllh bamasu tayar da hankali bane, dan jinjirai suna cikin k'oshin lafiya da kariyar ubangiji. Samha dai konan dacan bata matsawa, duk wani motsinta nakan yaranan, tazama bodyguard d'insu itada Ayusher da hajiya innaro, dan itamafa ta kafa ta tsare🤣. Mama Fulani dai ta danne zuciyarta tazo har sashen Galadima taga babies, harma suka samu k'yauta mai tsoka daga gareta. Ana gobe suna masarautar gagara badaufa tayi dank'am da jama'a, dan bikin suna na ban mamaki Sarki ya shirya, abin ba'a cewa komai. Inno ma dai wannan karon ba'a barta a baya ba, tazo masarautar su sunan tatta6a kunnenta, kuma 6angaren mama Fulani ta sauka😳😜. Koba komai zata kafa zata tsare, takuma raka ta jira🤸🏻‍♀😂 mana ga Mama Fulani. Harun da baya k'asar yayi tafiya a fannin aikinsa yau ya diro a Daren suna cikin masarautar, dama tun yana can labari yagama Isar masa Galadima ya samu y'an uku, Muftahu da kansa ya kirashi ya Sanar masa haihuwar, Yakuma tura masa hoton babies😽🤥 ***************** Wajen 8pm Galadima suka dawo daga masallaci sallar isha'i, shikad'ai ya shige falonsa, dan yana son magana da Munaya, gaba d'aya yinin yau tun safe daya Shiga bai samu komawa wajensu ba saboda hidimomi sun masa yawa. Ayusher ya kira, dan itama Munaya batazo da waya ba, lokacin da su Sauban zasu taho kuma basusan inda ta saka layinta Na Nigeria ba, sai sukaga babu amfanin d'akko wayarma. d'agawa Ayusher tayi, Galadima yace ta bama Munaya. Murya k'asa-k'asa tace bata da lafiya. Tashi yay daga kwanciyar da yayi, yace, “ciwon cikin ne dai?”. “eh shine wlhy Yaa Galadima ”. Dukda kunyar shiga mutanen yake dole ya mik'e ya fita, sashen nasu kam Alhmdllh da yawan jama'a babu laifi, ga yawan bayi da suka k'aru saboda inno da tawagarta, dukda ba'anan ta sauka ba. Tunda ya fito suketa gaisuwa da jama'a, wad'anda ma basu sanshiba yau sun gansa, musamman wasu a y'an uwan Munaya. cirko-cirko ya iskesu tsaye, Munaya Na kwance a gado ta cure waje d'aya da alama tanajin ciwon sosai, Aunty Mimi nata faman jijjiga yaron d'aya dake kuka. Duk kallonsa sukayi, cikin damuwa yace, “ciwon cikinne?”. Da eh suka amsa masa, ya taka zuwa gaban gadon ya zauna kusada ita, har zai ta6ata Mom tamasa nuni da a'a ya barta. dakatawa yayi shima ya zuba mata ido cikin tausayawa, gaba d'aya fita hayyacinta take idan cikinnan yana ciwo, kuma saida ta kwana biyu da haihuwa sanann yafara. ya tsira mata idanu ganin yanda take zufa, dukda garin akwai sanyin ruwan da akayi da yammaci. Yakai tsawon mintuna 30 a zaune kafin ya lafa mata, ahankali tafara gyara kwanciyarta tana mik'ewa sosai, da Galadima suka fara had'a ido, yace, “sannu”. Kanta ta d'aga masa cikin murmushin k'arfin hali, suma duk sukai mata sannu sauran. Nanma ta amsa cikin d'aga kai. Maganin da laraba ta tace a Kofi ta mik'o mata, Na gargajiyane, kar6a tayi ta shanye tana yamushe fuska, ta mik'a mata kofin sannan ta zauna sosai. Tausayinta ya kama Galadima, iyaye mata nashan wahala akan y'ay'a, ALLAH ne kawai zai biyasu. Ganin ta dawo dai-dai duk sai suka fita suka basu waje, bayan Aunty Mimi ta d'ora masa babyn a cinyarsa. Sannu ya kuma mata yana gyarama yaron kwanciya, murya a hankali tace, “ya daina ai, amma wlhy ciwon cikinnan yamafi haihuwar zafi”. ‘ta k'are maganar idonta cike da kwalla’. Tausayi ta kuma bashi, ya matso kusada ita sosai yana ruk'o hannunta, yace, “insha ALLAH Akash zai zo miki da Magani zuwa gobe, zai daina gaba d'aya ”. Kanta kawai ta d'aga masa amma batace komaiba. Kukan da macen tayi yasakasu kallonta su duka, nuni yamata ta d'auketa. Batayi musuba ta d'auketa ta saka a acinya, kamar jira suma sauran suka farka harna hannunsa, kai Munaya ta dafe tana fad'in “ni jikar fharuk ku shikenan da d'aya ya tashi kowa saiya tashi”. Murmushi yayi, “to basu birgeki ba ma, sunyo gadonku ne keda Munubiya, Ku ba haka kukayiba?”.. “a'a mukam ba irin wannan mukayiba yalla6ai”. “humm, ai inna ta sanarmin komai yarinya”. Da mamaki Munaya ta waro masa ido, ya d'aga mata gira yana kashe ido d'aya. 'Dauke idonta tayi cikeda basarwa. Shima saiya mik'e tsaye d'auke da yaron d'aya, ya kalli agogon dake a hannunsa sannan ya kalleta “inason ganinki”. daga haka ya sunkuya ya d'auki macen ya juya zai fita. “wai ina?”. ta fad'a da saurin dan karya fice. Juyowa yayi ya d'an kalleta, kamar bazaiyi magana ba sai kuma yace, “sashena”. bai jira cewarta ba yay ficewarsa. Kanta ta dafe tana sauke ajiyar zuciya, shi bama ya ganin gida cike da mutane, fitinar yalla6ai yawane da ita wlhy. batayi yunk'urin binsa ba, saima zaman shayar da Wanda ya bari tayi, harsu Samha suka dawo ganin ya fita. Shikam yanacan kwance a gado ya d'ora yaran saman cikinsa yana shafa bayansu, yayinda zuciyarsa ta tafi wata nahiyar tunani, ganin lokaci yaja bata zoba ya kalli a gogon hannunsa, shidai bazai kuma kiranta akan tazo ba, idan ta gadama kartazo. Mom data lura babu sauran yaran ta tambaya, cikin kunya Munaya tace, “suna wajensa”. Banbancin babba da yaro saurin fahimta, mom ta fahimci d'an nata yana buk'atar ke6ewa da matarsa, shiyyasa ya d'auki abinda dole tabishi inda yake ta kar6o.. Tace, “to aiko jeki ki kar6osu, dan shirin barci zan musu nima Na kwanta, gobe ba zama za'a samuba hidimomi zasuyi yawa”. Kamar Munaya tai ihu haka taji, to a aiki Ayusher da Samha su kar6osu mana, ai ba dole sai itaba, amma babu yan da ta iya, dan bazata iya sa6a umarnin Mom ba dai. Dogon hijjab ta d'auka ta zumbula, Mom kamar tayi dariya, a ranta tace, Munaya shi namiji ai ba'a hanashi yanda yaso, balle naku na yanzu da suke a fetsare ma. Harzata fice mom tace, “shima zoki d'aukesa”.. Ta kalli mom d'in tana fad'in “mom aikuma zasuyi yawa wajen d'akkowa”. “eh d'auka, basai ya tayaki ku d'akko ba”. Babu yanda Munaya ta iya dole shima ta dawo ta d'aukeshi, sai wani k'yallo idanu yakeyi Lamar yasan mi akeyi. Babu kowa a afalon, harma television an kashe, babu yanda ta iya dole ta nufi bedroom d'in, saida tayi sallama yabata izinin shiga sannan ta shiga. Harta zauna idonsa a kanta itada babyn hannunta, saiyaga ta k'ara masa k'yau ma da girma. Yace, “kin gama jan ajin? ai saki bari sai randa nazo tad'i ki jamin bawai yanzu ba”. Munaya ta ciza lips d'inta kawai batare da ta tanka masaba, Yaran ya kwantar gaba d'aya, sannan yatashi zaune yana fad'in “taso”. “intaso kuma, ba magana kace zamuyi ba? please ka fad'a a haka”. ta fad'a kamar zatayi kuka, (Dan hirar innaro da laraba ta tuna da sukace jiya wata yarinya sati biyu da haihuwa ta yarda da mijin saiga ciki ya fito yaro Na wata uku, ciki wata biyu da sati biyu🤣, itama fa yanzu kaffa-kaffa zatakeyi da Galadima, inma baka badaba sai'a saka maka k'arfi🤭😂). Tsaf Galadima ya fahimceta, dan haka yay wani miskilin murmushi yana fad'in “oh kina min bak'in cikin sake ajiye abin cikin kwan ne?”. Sosai Munaya ta waro idanu, a firgice tace, “ban ganeba?”. “Zaki gane lokacin da kika zo hannuna”. Ta yunk'ura da sauri ta mik'e, ita tama manta da yaro ajikinta, ALLAH dai ya kiyaye tai saurin tarboshi, Galadima ma dirgowa yay daga gadon, saidai kawai ta gansa kusada ita. Rungume yaron tayi tana sauke ajiyar zuciya, gashi mai kamar mara lafiyarne. Shima Galadima had'ata yay itada yaron ya rungume, ganin haka saita mik'a masa shi ita ta janye jikinta. hannunta ya rik'o ya maidota, daga k'arshema janta yay zuwa gado, ya zaunar da ita shima ya zauna, fuskarsa babu walwala yace “Munaya badai haka kikemin ganganci da yaraba?”. A tsorace ta girgiza masa kai idonta Na cika da kwalla, “wlhy yalla6ai a'a, yanzu ma Na shafa'ane”. Taune lips d'insa yay tayi yana kallonta, haushima ya hanashi samo amsar bata, jima yake kamar ya maketa, anya zaibar yarinyarnan zuwa wani wankan banza can, taje tamasa wasarere da yara?. Yanda ya koma duk saitaji babu dad'i, shi yaronma bafa kuka yakeba, yad'an dai firgita ne kawai yay kamar zai shid'e. Saida ya gama cikarsa da batsewa sannan yay kwafa, ita shima abin yabata mamaki, shikenan yanzu y'ay'ansa kawai ya Sani, mutum bazai ta6a iya kuskure ba a Kansu saiya hauma mutane bala'i, shin ya fita sonsune itada tasha wahalar d'aukar ciki da haihuwa?. Kwantar da yaron yay yanata wani had'e fuska, itama tasha kunu ta shareshi. K'aton akwatin dake gefensu ya matso dashi, kayane Na jinjirai masu k'yau da birgewa, Wanda kallo d'aya zaka musu Kasan Na musamman ne, kala-kala ne amma kowanne set uku ne, abinda ya banbanta su wannan Na macene wannan Na mazanne. kowanne da takalma abindai masha ALLAH. tsaf Munaya ta gama gani, ta kallesa tana fad'in “Sunyi k'yau”. Yana basarwan nan tasa yace, “wanda zakuyi amfani dashi gobe ne, idan akwai abinda bai yiba saiki fad'a da safe a nemoshi, ga naki nan kema”. ‘yay maganar yana nuna mata d'ayan akwatin’. Jawowa tayi ta bud'e, duk an d'inka kayan, kayane masu tsadar gaske Na mace y'ar gata, bama tasan ta rungumeshi ba Dan dad'i, sai jero masa godiya da addu'oin fatan alkairi takeyi. Shima tuni ya manta da fushin ya rungume kayarsa yana murmushi. cikin kunnenta yace, “kinfi k'arfin komai a wajena friend dan kin gamawa Muhammad Sameer komai”. Munaya ta murmusa tana d'an dukan k'irjinsa, tace, “kana shamin k'amshin ne nagama maka komai?”. Hannunta ya rik'e yana murmushi, yamatso da fuskarsa gab da tata, murya k'asa-k'asa yace, “ke d'ince Zuma ce...... ” Harar data dalla masa ta sakashi fasa k'arasawa ya wani basar yana kashe mata ido d'aya, “dad'ina dake akwai mazurai, gaki babu k'arfi ga tsoron tsiya”. Munaya tayi dariya, “aka gaya maka banida k'arfi? kabari nakuma samun lafiya sai a gwada kwanji”. Wata dariyar mugunta Galadima yayi yace really?”. “yes” ta fad'a cikeda karsashinta. Ya mik'a mata d'an yatsansa alamar su k'ula. Babu musu tabada nata itama suka k'ula. Murmushi yaytayi saboda muguntar dayasan yana shiryawa, wadda ita Munaya bata fahimci komaiba a ciki saboda wauta.🤣 *_Washe gari_* Ta kasance safiyar suna, inda aka rad'a sunan yara bayan sallar Asubahi, *_Abdurrahman, Abdurraheem, and Amaturrahman_* masha ALLAH Babies ALLAH ya raya Ku akan sunnah da tafarkin addinin Islam. Yara sunsha Addu'oin fatan alkairi sosai, tun kuma a safiyar shagalin suna ya fara, dan kowa yana cikin walwala da farinciki, mai jego munaya ansha k'yau itada babies har an gaji, kamar ka sacesu ka gudu, hotuna dai suna shansu kala-kala a yau d'inan, Su Momma ma da basa kusa anata sambad'a musu, dan duk wani motsin da za'ayi Sauban da Samha basa gajiya da tura musu, sai sukaji tamkarma suna nan suma, saboda kallon komai suke tamkar live, farin ciki da walwala sun yalwatu a zuciyar Abie, bakinsa yakasa rufuwa dan tsabar nishad'i daya tsinci Kansa yau aciki. Hummm babbar magana, kayan barka dai sun iso, fans yaufa nasha kallo, kaga Inda akeyi don ALLAH, ta bakin Munaya tace INA zasu da wad'annan kaya haka, lamarin tamkar fariyya, gashi kowanne sashe sai kawo nasu sukeyi, gidan sarauta manya, babu Wanda zaiso aga kasawarsa, ballema wannan kana k'inyi za'a CE bak'inciki kakeyi, shiyasa mama Fulani aka ware aka zuba kayan barka Na gani Na fad'a, daga gidansu Munaya ma su inna sun taka rawar gani dai-dai k'arfinsu, daga ita har Munubiya komai iri d'aya aka musu, kayan babies ne kawai Na munaya yafi Na munu saboda su su uku ne ita kuma Nata biyu. Nanfa y'an gidan suka Shiga k'us-k'us d'in gulmar Ina inna ta samu kud'in yin wannan hidima haka? dansu basuyi zaton hakanba, musamman da abin yazo da yawa ma, itadai inna ma ko kallo basu isheta ba, hidimar gabanta da farincikin datake cikine a gabanta, bakinta yakasa rufuwa saboda farinciki da godiyar ALLAH mai sassauya al'amura a yanda yaso a kuma lokacin da yaso, idan ALLAH ya jarabceka karkayi bak'in ciki, hak'urinka zai iya zama sauyin alkairi a gareka, inama iyayensu Nada rai suga wannan k'yak'yk'yawar rana, ta share hawayenta tana murmushin farin ciki, sannan ta kira y'ar uwarta a waya suka cigaba da tattaunawa. ***** K'arfe uku da rabi kuma za'a gudanar da gagarumar walima da aka kama babban hall Na musamman. A wannan rana yara dai har fada aka kaisu sukayo gaisuwa da hotuna da mai martaba da gayyar y'an uwa da abokan arzik'i, su Harun dai sune gaba-gaba, uban gayya kuwa Muhammad Sameer Saifudden Galadima Baban y'an uku😂 ai ba'a cewa komai, koma ganinsa ba'ayi saboda tsabar shiga hidima, wannan suna ko bikidai iyaka kenan. Nasan kuma fans duk kunyi shirin wannan walimar baje dad'i😋😋. Nifa buhu Na tanada walle😆, saura kuce Bily tacika zari da son banza kuma🙄, har y'an anguwarmu saina kar6oma gifts d'insu😜😂🤸🏻‍♀. **************** Alhmdllh yaran Mununbiya ma an rad'a musu suna bayan sallar Asubahi, Namijin *_Aminudeen macen Ameenatu_* ALLAH ya raya wad'annan yara masu albarka😘😘🥰. Yau daikam farin cikin da Abba da innarsu suke ciki 6ata lokacine ma, kai da dukkan masoyansu irinmu, masu bak'inciki kam Ku k'ara himma, hassada ga mai rabo takice😏🤷🏻‍♀. Kowa nabashi dama ya k'iyastama zuciyarsa yanda bidirin suna yake guna, dan Alk'alamin Bily yau yayi k'ank'anta wajen wallafowa, sai mugama Na wannan satin bikin sunan bai k'areba😁.................✍🏻 Kuyi manage da wannan yau inada uzuri🤦🏻‍♀. ☺my Guy's a kafta kawai danjin yanda bikin suna zai gudana gobe idan ALLAH ya kaimu, kowa dai ya k'ure adaka dan karfa a kawo mana raini😕, kunsan dai halin mama Fulani, tana iya hanawa abarmu shiga😩🥺. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣5⃣ ................Aunty Salamah da kanta tazo yima Munaya kwalliyar zuwa wajen walima, saida tafara biyawa tama Munubiya sannan ta wuto nan, ta iske su duk a damuwar kukan da Abdurrahman ketayi, sai faman jijjigarsa akeyi amma yaro yak'i yin shiru, an basa nono yak'i kar6a, innro ta kar6esa ta hura masa kunne, ya kuma k'yak'yacewa da sabon kuka yana dunk'ulewa waje d'aya, tace “inaga kunnensa ke ciwo yaronnan”. Munaya Na gefe zaune ta zuba tagumi kawai tana kallonsu, ita kad'ai tasan suyar da ranta ke mata, gashi Galadima baisan wainar da ake toyawa ba, yanacan tareda su Akash da suka iso yanzu. Innaro ta dungureta, d'ago idanu tayi ta kalleta, ta mik'a mata Abdurrahman daketa sauke ajiyar zuciya, “d'iga masa ruwan nono kad'an acikin kunnen insha ALLAH idan aka dace zai daina”. Kar6arsa tayi, ta d'ora kan cinyarta, dukma ta rikice ta rasa yanda zatayi, saboda sai mimmik'ewa yakeyi azaba na cinsa, ga Amaturrahman itada Abdurraheem suma sun d'akko nasu kukan, laraba ta rik'e matashi ta samu ta d'iga masa, ruwan nonon Na shiga yakuma mimmik'ewa yana kwalla ihun sabon kuka. Saiga hawaye a na zuba a idon Munaya, tasaka hannu ta toshe kunen ta kozataji sassaucin jin kukan nasu dake d'aga hankalinta. Tausayinta saiya kama laraba, tasan indai wannan ne yanzu ma aka fara, yaro d'aya ma ya kake k'arewa balle yara uku. Cikin amincin ubangiji kuma duk sai sukayi shiru, innaro da laraba sunata faman jijjiga, itama Aunty salamah ta kar6i Na hannun munaya, tun suna ajiyar zuciya har barci ya kwashesu. Munaya ta shige bayi tana share ragowar hawayenta. Baki innaro ta ta6e tana fad'in “lallai aiki yasamu mata, yo indai kukane yanzu ma kika fara”. Daga Aunty salamah har laraba dai babu Wanda ya tanka. Munaya kuwa data jiyota daga bayi tace “aniyarki ta biki, mai mugun fata kawai”. Wanka tayo ta fito, Aunty salama kawai ta tarar a d'akin sai bayi biyu dake morping, suka durk'ushe k'asa suna gaida Munaya. Hannu ta d'aga musu kawai dan batasonyin magana, har yanzu raunin tausayin Abdurrahman baibarta ba. ta kallesu duk suna kwance kan gado barci ya d'aukesu, yayinda Aunty Salamah ke zaune kan sofa tana warema yaran kayan da za'a saka musu. Ta d'ago ido tana kallon Munaya, “haba auta kuka kikayi da gaske? Please kidaina musu kuka, ba'ason uwa Na zubarma d'a hawaye dukda wannan Na tausayine kinji”. Munaya ta had'iye abinda yamata tsaye a mak'oshi tana gyad'ama Aunty salamah kai. Saida Aunty salamah ta gama ware kayane sannan ta taso suka fara kwalliyar, anutse sukeyin komai, dan da sauran time, hakama Munubiya a nutse aka mata tata, anama Munaya tana kallon hotunan Munubiya, taji dad'in yanda y'ar uwarta tasha k'yau, dukda ma batakai ga saka kayaba. ★★★★★★★★★★★ Muftahu nata kai kawo a tsakar d'akinsa, tunanin tawace hanya zai fargar da Galadima kawai yakeyi, dan dolene saida hannunsa zaiyi wannan aikin, saboda had'arinsa, gudun kar reshe ya juye da mujiya, sannan aikin yana buk'atar takune da sirri. Fitowa yay yanufi can cikin k'aton lambun masarautar indasu Galadima suke tareda mafi yawan y'ammata da samarin masarautar. Wasu sunata hirarsu in group, wasuko hirar tasu ta masoya ce, Muftahu ya k'araso inda su Galadima suke, sun baza babbar darduma anata hira, Bama zaka ta6a Sanin suna lambun ba saboda sunacan ciki nesa da sauran yaran. Galadima na zaune a gefe cikin kujera, ya d'ora k'afafunsa a wata kujerar, sanye yake da farar shadda d'inkin boda, fuskarnan babu walwala ko kad'an, gaba d'ayan hankalinsa yanaga system d'in daya d'ora bisa cinya yana latsawa. Muftahu ya mimmik'a musu hannu sukayi musaba cikin fara'a. Amma tsakaninsa da Harun ba hakan baneba, kowa murmushi mai cikeda ma'anoni yay ma d'an uwansa, kafin su saki hannun juna. Muftahu ya matso kusada galadima shima ya bashi hannu sukayi musabaha, k'aramar takardar dake mak'ale a hannunsa ya sakarma galadima a hannu. Kallonsa galadima yayi, sai yay masa murmushi yana signal da ido alamar ya duba. Galadima bai ce komaiba ya cigaba da abinda yake ya basar da takardar. Muftahu kuma ya koma cikin su Harun aka d'ora hira, tamkar babu abinda ke damunsa. Galadima baibi takan takardar da Muftahu ya basaba har tsawon wasu adadin mintuna, sannan ya bud'e ya duba. _Ranka ya dad'e ina buk'atar muyi magana kafin a zauna wajen walima, magana mai muhimmanci please._ Iya abinda ke jikin takardar kenan. Galadima ya d'an ja eyeglasses d'insa k'asan ido ya kalli Muftahu, cije lips nashi yayi yana janye idonsa. Ya sauke k'afafunsa yana d'ora laptop d'in saman kujerar, ya d'auki ruwan gabansa yana sha da maida hankali garesu. jin hirar tasu ta y'ammata ce sai ya zuba musu ido kawai bai saka bakiba, dan shi dama ba'a wannan hirar dashi tun can da, suma duk sunsan haka, shiyyasa ko suna shirmensu basa sakoshi. Ganin zasu saka masa cinwon kai saboda hayaniyarsu Na Neman yin yawa saiya mik'e d'auke da Laptop d'insa. Duk kallonsa sukayi, Zayyan yace, “ina zuwa daddyn Triple's?”. K'aramin tsaki yaja, da k'yar ya bud'e baki yace, “zaku samin ciwon kaine, zanje nad'an huta kafin time yayi”. ya k'are maganar da kallon agogon hannunsa. Matawalle yay murmushi yana salute nashi, shima murmushin ya masa yana kaimasa rankwashi, ya kauce gefe yana murmushi, (dayake shima bai cika hayaniya ba). Wuce warsa yay cikin takun nan nasa Na izza da k'asaita, da sauri wasu yaran masarautar dasuka had'a tasu dabar agefe biyu aciki suka taso suka k'ar6i laptop d'in hannunsa saboda girmamawa, ya mik'a musu yana murmushi, yana gaba suna binsa a baya, sai zuba masa surutu suke akan shagalin daza'a sha yau, shidai murmushi kawai yake musu babu magana, basu damuba, dan kowa yasan halin galadima a masarautar nan, haihuwar nan ma wasu da yawa zasu iya cewa sunga hak'oransa a waje. duk inda suka gitta ana kwasar gaisuwa, bayi kam zubewa suke domin girmamawa a garesa. Har sashensa suka masa rakkiya, sarkin mota ya kar6a laptop d'in ya k'arasa masa da ita zuwa ciki.. Baibi ta ainahin k'ofar da zata kaishi babban falonsu ba, saiyabi wata k'aramar k'ofa da kai tsaye nasa sashen zai shige basai mata y'an suna sun gansa ba. A falo ya iske Sauban kwance yana barci, da alama yagama yawonsa ne gajiya ta makesa, da kallo Galadima ya bisa, amma dan ya tabbatar da lafiyarsa saiya d'ora yatsunsa biyu a wuyan Sauban d'in, babu zafi, ya maida goshinsa saiyaji zafi sosai, Galadima ya girgiza kai, yasan dama ba lafiyace zata saka Sauban barci a irin wannan lokacin ba ana wannan hidimar. Bai tasheshi ba ya shige cikin bedroom, zama yay a bakin gadon yana cire bottom d'in rigar guda uku, ya huro isaka daga bakinsa yana zamewa ya kwanta batareda ya cire rigarba, zuciyarsa tana ta jujjuya mi Muftahu yake nufi ne? wace magana zasu tattauna?. waya ya jawo da nufin kiransa, sai kuma ya fasa, jefar da wayar yayi yamik'e yana ida cire kayan gaba d'aya. ya shige wanka. ya ja adadin wasu mintuna masu tsayi kafin ya fito sanye da bathrobe fara sol, sai k'aramin towel a hannunsa yana goge fuskarsa zuwa wuyansa. Yana tsaye gaban mirror zai fara shafa mai ya jiyo ana knocking d'in k'ofar falonsa, Computer d'in daya ajiye wadda yake kallon kowane 6angare na sashen daga cctvs cameras d'in daya zagaye ko ina, tun zuwan dayayi Na k'arshe ya saka akayi masa wannan aikin, sannan ya d'auki mataki akan waccan cctv d'in da Munaya tamasa hannunka mai sanda da ita. Sarkin k'ofa ya gani, sai kuma Muftahu daga can waje alamar yana jiran iso ne. Guntun tsaki Galadima yayi, ya fito zuwa falo, Sauban dake barci ko motsi baiyiba balle yasan ana knocking d'in. yana daga tsaye yabama sarkin k'ofa izinin shigowa. Cikin girmamawa yace, “ranka yadad'e yalla6ai Muftahu ne ke Neman iso”. Da hannu Galadima ya masa nuni da ya shigo. Sarkin k'ofa ya amsa da to sannan ya fice. Komawa Galadima yay ciki yacigaba da shafa mansa, saida ya gama tsaf sannan ya zira jallabiya Brown ya fito. A falo ya iske Muftahu zaune yana control d'in television da remote. Galadima ya zauna a kujera mai zaman mutum d'aya, sai wani d'aure fuska yake. Muftahu bai wani damuba, dan yariga ya saba da wannan ai. Kallonsa Galadima yayi cikin lumshe ido yana fad'in “Mike faruwane?”. Ajiye remote d'in Muftahu yayi, ya kalli Sauban dake barci. d'an ta6e baki Galadima yayi, yace, “karka damu, kayi maganarka kai tsaye kawai”. Cikin jinjina kai Muftahu yace, “Ok, babu abinda ke faruwa saidai shirin faruwar kam, Ranka ya dad'e bamuda isashen lokacin wata magana mai tsawo yanzu, saidai ga wannan takardar ka duba, so yanzu wannan ne akan ga6a, shine yakamata mu d'au mataki akansa, daga baya komi kenan namaka alk'awarin warware makashi, fatana dai ka fahimci wannan d'in saboda had'arinsa”. Kar6ar takardar Galadima yayi, ya d'auki medical glasses d'insa daya ajiye a teble glass d'in dake gefen haggunsa ya saka, duba takardar yay a tsanake, cikin wani yanayi dake nuna tsantsar tashin hanki yace, “Muftahu wannan maganar gaskiya ce kokuwa? karkamin wasa da hankali a wannan karon dan bazan d'aga maka k'afa ba a wannan ga6ar alwashi nane”. Murmushi Muftahu yayi, ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in “Nabaka wannan damar, inhar kayi gamo da sa6anin hakan karka barni da numfashi ranka ya dad'e”. Wani shegen Murmushi Galadima yayi, yamik'e d'auke da takardar ya koma bedroom batare da kuma kallon Muftahu ba. Tausayin Galadima ya kama Muftahu, mik'ewa yay shima ya fice. Jefar da takardar Galadima yayi akan gado yana taune lips nashi tamkar zai huhhudashi, wata irin suya zuciyarsa ke masa, lallai dolene ya jinjinama Munaya, dan ta taka rawa wajen shagaltar dashi wanene shi? minene burinsa?, ganin tunani bazai masaba yatashi jikinsa Na rawa yafara wasu had'e-had'en abubuwa, waya ya d'auka ya kira Ayusher, ta d'aga cikin hanzari tana mik'ama Munaya dake shayar da Amaturrahman data tashi daga barci tana kuka. Kallonta tayi da mamaki tace, “wace Ayusher?.......”. Galadima ya katseta da fad'in “ki kawomin kayanda su Abdurraheem zasu saka”. iyakar maganar da yay kenan ya yanke wayar yana cigaba da latse-latse, zuwa can kuma ya ajiye ya mik'e yana cire jallabiyar jikinsa. Baki sake Munaya tabi wayar da kallo, mike damun galadima haka? Muryarshi irin wadda tasan asalin galadima ce, hakan na nufin akwai matsala kenan? to mine zaiyi da kayan da yara zasu saka?. batada mai bata wad'an nan amsoshin dan haka ta mike tana ajiye Amaturrahman d'in, aiko ta fashe da kuka an cireta bata k'oshiba, tsaki Munaya tayi tana fad'in “ai saikiyi tayi, ku matsala ubanku matsala mutum yarasa wazai kama. Ayusher da Aunty Salamah suka kalli juna suna gumtse dariya. Gyale taja ta lullu6a, dama tasaka doguwar rigar matirial kafin dai time ya k'arasa. ganin zata wuce yarinya na kuka Auntu Salamah tace, “dawo ki d'auketa mana, idan kinje can saiki bata nonon”. Tamkar Munaya zata saka kuka haka ta dawo ta kwashi Amaturrahman ta fice tana k'unk'uni. A falo ta iske Sauban Na barci, wucewa tayi cikin bedroom d'in kanta tsaye, amma saida tayi sallama ya bata izinin shiga. Tun da ta shigo taga yanayin da yake sai gabanta ya dad'i, tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki ta mik'a masa ledar data zubo kayan sannan ta zauna a kunyace saboda yanayin da yake babu kaya. Ba tare da ya kalleta ba ya hau Fiddo kayan, ya zubesu saman gado yana d'aukar hotonsu a waya, yay latse-latse nawasu mintuna kafin yasaka wayar a kunne. “Saleem ka dubamin kalar kayannan, koda basu kaisu tsadaba, yanzunan kataho ka kawominsu”. Bataji mi Saleem yafad'a daga canba. Muryarta a raunane tace, “yalla6ai mike faruwa wai?”. Jajayen idanunsa ya d'ago ya kalleta, k'ala baice mataba ya mik'e ya d'akko wani k'aramin box ya dawo ya zauna, ita duk saima kunya takuma kamata, saboda dagashi sai boxer, amma taga ko a kwalar rigarsa bai damuba, hidimar gabansa kawai yakeyi. Kwantar da Amaturrahman tayi kusa dashi ta tashi zuwa wardrobe d'insa, k'aramar t-shirt ta d'akko, tazo ta mik'a masa. Ya d'ago ido yana zuba mata harara, dukda ta tsorata saita daure tace, “please mana yalla6ai”. tayi maganar muryarta a raunane. Saida yayi k'aramin tsaki kafin ya amsa ya saka, wani abu da batasan minene ba taga yana mak'alawa jikin kayan yaran, saida yagama tsaf sannan ya maidasu a ledar, kallon Amaturrahman dake k'yalla y'an idanu zata fara k'aramin kuka yayi, ya shafa kumatunta batare da ya d'auketa ba. Laptop d'in sa ya jawo ya saka eye glasses d'insa, ya kalli Munaya yamata alama da ido akan tazo. Babu musu ta taso zuwa kusa dashi ta zauna. Laptop d'in ya d'ora mata akan cinya yace, “wanene SD a cikin su?”. Nutsuwa Munaya tayi tana kallon hotunan, cikin waro ido tace, “kai ga Fu'ad ai”. Da mamaki Galadima yace, “Fu'ad!?”. “eh wlhy yalla6ai, Wanda ya kaimu birnin gayu plaza ranar da abunnan ya faru”. Kar6a laptop d'in Galadima yayi yakuma kallon hoton da k'yau yana taunar lips, kuma mik'a mata yayi batare da yace komaiba. itama batace dashiba tacigaba da bin hotunan da kallo sannu a hankali. Harta kai k'arshensu babu SD. ta kalleshi cikin damuwa, “yalla6ai babushi fa anan gaskiya”. Kansa ya jinjina mata yana kar6ar laptop d'in, cigaba yay da danne danne, itadai Munaya tana kallonsa. Kuma d'agowa yay ya kalli Munaya, “duba annan kuma fa”. Kallon hotunan ta shigayi, canko saiga hoton SD, tace, “Alhmdllh gashi anan”. Kallon hoton Galadima yayi, da mamaki yace, “kinsan wanene wannan kuwa?”. “Ah! yalla6ai SD ne mana”. “Munaya kin tabbata wannan ne kika gani a wajen Abba?”. “Wlhy shine yalla6ai, bazan ta6a manta fuskarsa ba ai komai dad'ewa. balle acikin abinda bai rufa 2years ba, amma kasanshi ne?”. Bai iya cemata komaiba, sai zuciyarsa dake wani irin bugawa da sauri-sauri kamar zata fad'o, mamaki ya hanashi motsin kirkirma, Alhaji Shehu Darma shine SD kenan, babban Amini kuma d'an uwa ga Mahaifin su Samha, innalillahi, ya abubuwa keneman koma masa rikid'ar hawainiya haka?, wannan fa Fu'ad d'in d'ane ga yayar Uwargidan Sarki mahaifiyarsu Matawalle, cikin cije lips ya buga hannunsa akan gadon yana fad'in “Kai!!!! miyasa hakane? miyasa duk Wanda Na yarda dashi shike fara bayyana a maicin dunduniyata?!! miyasa rayuwa tazomin da irin wannan rikicin ne?, oh God!!”. ‘ya k'are maganar cikin matsanancin k'araji, tareda runtse hannayensa waje d'aya. Tsoro ya kama Munaya, ganin yanda duk ya rikice kamanninsa suka canja, idonsa yayi matuk'a jajur, jijiyoyinsa da gashin jikinsa duk sun mimmmik'e, ga Amaturrahman data tsorata lokacin daya buga gadon, d'aukarta tayi tahau jijjigawa. Sauban ma a firgice ya tashi, ya hau waige-waige, ganin babu kowa a falon saiya nufo hanyar bedroom d'in Galadima, tabbas muryarsa yaji a yanayin da ba'aso. harzai murd'a k'ofar saiya fasa saboda jin kamar muryar Munaya tana magana. Tunda tasamu Amaturrahman tayi shiru sai ta d'auki towel d'insa ta goyata, ta matsa kusadashi a tsorace, hannunta ta d'ora akan nasa daya dafe mirror, ko motsi baiyiba balle ya kalleta. Murya a d'arare kuma a sanyaye tace, “please yalla6ai, fushi baisa a samu sauk'i saidai ya k'ara zafi, kaine kasha gayamin wani karatun baya buk'atar fassara ko dogon nazari, akan barsane kawai a yanda yazo, dukda bansan tushen matsalarba zan iya bada gudunmawa wajen kama bakin zarenta, kayi hak'uri ka kwantar da hankalinka, ita fahimta fuskace, ba fushinka ko tsantsar damuwa ne abin buk'atarba yanzu, d'ana tarkon dazai fara kamo maka hannun mak'iya shine jarumta, ka danne kuma ka daure, ni dama Dan banida ikon hana walimar nanne kawai, amma inaji a jikina akwai lauje cikin nad'i, saidai wad'anda suka nad'a d'inne bamuda ilimin saninsu sai ALLAH yaso Samar damu, amma ai duniya makarantace, idan su a can suka yini kaikuma saika nuna musu kwana kayi, lokuta da dama fushinka ke lalata maka aiki, dan inhar kana cikin fushi dukkan aikinka tafiyar hawainiya yake, wannan lagon naka suka samu suke wasa da hankalinka, koda ace wani ya salwanta cikin yarannan karka d'aga hankalinka, ALLAH n daya baka yafika sanin hikimar k'addara hakan, duk lokacinda kaga Matsaloli sun raunana, buk'atu kan kuma kan yalwata ne, kasa a ranka wannan wata damace tazo gareka, ai duk lokacin da aka rasa kwallo a cikin wasa, ba wasan ake dainawa ba, wata kwallon ake jehowa a cikin fili”. Duk maganar da takeyi ko motsawa baiyiba, baikuma juyo ya kalleta ba, saidai alamu sun nuna yana saurarenta, ta janye hannunta ta juya zata fita tana hawaye. Cak ta tsaya saboda rik'o hannunta da yayi, kusan minti 1 suna a haka, ta waigo ta kallesa, har yanzu yana a yanda yake, kallon hannunsa daya ruk'o nata tayi. Bai kalletan ba kuma bai saki hannunba yace, “Lallai ina shaidama dukkan Wanda ya maida rayuwata data ahalina magijin kallonsa, zan tsiyayar masa da idanun, sannan zan kacaccala rayuwarsa Na binnesa da ransa”. ya mik'e tsaye sosai tareda juyowa ya jawo hannunta ta fad'o jikinsa, saurin dafe Amaturrahman dake bayanta tayi da d'ayan hannun. Ya saka idonsa dasuka firgitata cikin nata, fuskarsa dab da tata yace, “kedai kibama yaranki kariya kawai, dan sune fitilar zuciyar mijinki”.. sakin hannunta yay ya zagayeta yabar wajen. Tamkar sokuwa haka ta bisa da kallo, yayinda zuciyarta keta kuma maimaita maganar tasa, _yaranta, kuma mijinta?_ mi yake nufi to?, amsar itace bata saniba. Jitai kawai ya saka mata ledar kayansu Abdurraheem a cikin hannu, baice k'alaba yabar wajen zuwa gaban wardrobe d'insa yafara fiddo had'add'iyar Shadda gizna ash colour, sai maik'o take da d'aukar idonu. Ganin ya shareta yana cigaba da hidimarsa itama saita juya ta fice. Tunda Sauban yaji motsin kama handle d'in k'ofar yabar wajen da sauri. Fitarta babu dad'ewa Saleem ya kawo kayanda Galadima ya umarcesa. __________________________ Munaya Na komawa Aunty Salamah tahau shiryata, dukda taga a yanayin data dawo bata tambayeta daliliba, saida tagama gyara mata fuska tana gyara mata gashi Munaya tafara fad'a mata iya abinda taga ya dace kawai Aunty Salamahr ta iya Sani, sauran kuma sirrinta ne ita da mijinta. Murmushi Aunty Salamah tayi, tace, “dukda banida tabbacin faruwar wani Abu dagani har Munubiya dama mun shirya hanyoyin d'aukar matakai saboda tsaro, kowa baisan dalilin Munubiya na dagewa akan ki dawo gida ki haihuba, amma ita tasan dalilinta, ba son zuciya ya sakata yin hakanba, Ubangiji Na kallon kowa kuma zaiyi maganin komai, tun a shekaran jiya Saleem yazo mungama tsara komai dama, kuma ya tabbatar min Muftahu yasan komai dan yaga alamar shima tsaye yake da k'afafunsa, inaga yau dai shine yabama Galadima satar amsa, kuma hakan da yayi shine dai-dai, saboda duk abinda zai faru a yau d'innan shi Galadima zai fara zargi”. Munaya tace, “hakane Aunty Salamah, shiyyasa wlhy Muftahu yafara bani tausayi, ALLAH ya kawo ranarda zai wankesa ayi walk'iya aga kowa dai”. Amin ya rabbi gimbiyar Galadima Sameer, ku kwantar da hankalinku, komai kam ya taho gangarar zuwa k'arshe, dan alamomi suna nuna haka”. “nima inajin haka a jikina Aunty Salamah”. Da wannan hirar aka gama gyaran kan tahau shiri cikin less d'inta Ash colour irin kamar kayan da Galadima zai saka kenan. Hummm masha ALLAH, maganar k'yawun da Munaya tayima 6ata lokacine, amma tayi k'yau. Yaranma tsaf aka gama shiryasu, abin kamar ka sacesu ka gudu, sunyi fes. Kowa yagama hada-hadar shiri, ana fitowa daga sallar La'asar za'a fara kwasar mutane zuwa hall d'in da aka tanada. *_4:00pm_* Dukkan mai ruwa da tsaki akan wannan taro ya hallara a gaban motocin da za'a kwashi jama'a, ana fitowa daga salla kuwa aka fara tafiya. Munaya dai tana d'aki bata fitoba, hakama Galadima saida ya dawo salla sannan yafara shiri ma shi. Saida kusan kowa ya tafi sannan iyayen gayya suka fito. Munaya ce tafara fitowa, kuyangi Uku Na d'auke da yaran a bayanta, yayinda wasu kuma ke take mata baya, a babban falon sashensu suka tsaya jiran fitowar Galadima. Tunkan ya fito daddad'an k'amshinsa ya fara isowa, saikuma sautin takun takalminsa wanda tarihi yaso maimaita kansa ga munaya, dan takun nasa Na daidaituwa ne da bugun zuciyarta. Yana gaba Sauban na binsa a baya, Tunda ya fito Kuyangin duk sukai k'asa da Kansu, yayinda ya k'araso sai suka zube k'asa suna kwasar gaisuwa, hannu kawai ya d'aga musu, idonsa akan Munaya wadda itama ta risinar da idonta tana masa kallon k'asan ido. Ba k'arya yayi matuk'ar k'yau, komai nasa Ash colour ne, kuma kayan sarauta y'an asali, harda rawanin daya kuma fiddi ainahinsa Na jinin sarauta, rawanin ya sakaya sajensa hancinsa zuwa bakinsa kawai ake iya gani, idanunsa na cikin eyeglasses dabaka isa kaga kwayarsu ba, dan ya toshe su 6am. Juyawa yay ya kalli Sauban dake gefensa, Sauban ya fiddo Alk'yabbar dake cikin bag d'in hannunsa ya mik'a masa, kar6a galadima yayi yana mik'ama Sauban had'ad'd'iyar sandar hannunsa da zaka iya d'auka ta gold ce, ya warware alkyabbar ya matsa gaban Munaya dake tsaye har yanzu, yayinda kuyanginta ke a dur kushe har yanzu suma. Matsawa yay jikinta tamkar zai rungumeta, k'amshin turarensa ya cika hancinta ta lumshe idanu, ya sako alk'yabbar ta bayanta, Sauban na gefe yanata zuba murmushi da d'aukarsu hoto. Tamkar sokuwa haka Munaya ta tsaya har Galadima ya gama saka mata alk'yabbar a jiki, ya juya Sauban yakuma bashi turaren dake cikin jakkar, feshi ya shiga yimata da turaren, zuciyarta sai kaikawo take yi na d'umbin mamaki da al'ajabin wannan salo, Bayan ya gama ya maidawa Sauban turaren yanama Munaya nuni da suje da hannu. Haka suka fito a jere Kuyangi na take musu baya, yayinda Sauban yake gefe yanata zuba musu hotuna a Camera. Motar da Sarki ya bada ita aka bud'e musu suka shiga, Sauban ya kar6i yaran d'ai-d'ai ya mik'a musu, sannan ya shiga gaba kusada sarkin mota da Amaturrahman shima. Motar ta d'auki shiru tamkar babu wani mahaluki mai numfashi, Galadima ya zubama Abdurahman dake hannunsa ido kawai yana kallo, yayinda ya sak'ala hannunsa d'aya cikin Na Munaya yana murzayatsuna a hankali. Itama dai tayi shiru sassan jikinta Na kar6ar sak'on ninsa. A haka suka Isa har cikin harabar hotel d'in, Wanda ya cika dank'am da motoci, duk Wanda yagani yasan yau taron Na manyane, kodan tsaro Na musamman da wajen ya samu tundaga farkon Layin da hotel d'in yake. Sauban da Sarkin mota suka fito, ba'a bud'e su Munaya ba, kalonta Galadima yayi fuskarnan dai babu walwala har yanzu, batareda yayi maganar ba ya kamo kwalliyar zaren gaban alk'yabbarta ya matso da fuskarta kusa da tashi, ta bud'e baki zatai magana ya d'ora nashi. Saida ya shanye jambakin lips d'inta tas sannan ya saketa yana zuba mata harara. Idonta harsun tara kwalla, cikin lumshe idanu da k'asaitacciyar muryarnan tasa mai had'e da izza yace, “Sau d'aya nake gargad'i, karki bari nasake miki na uku akan fita da lipstick a baki”. ya k'are maganar da kad'a mata yatsansa. Wani yawu Munaya ta had'iye kawai tana jinjina masa kai, wannan ikon ikoko yana bata mamaki, shiyyasa fa tace Aunty salamah ta saka mata janbakin kad'an, gashi yamata k'yau amma tsabar mugunta ya shanye, lips d'insa sai zafi yakeyi, ta harari Abdurraheem dake cinyarta, saikace shine yayi laifin🤭😂. Bud'e musu akayi suka fita, Samha da Ayusher suka kar6i yaran. Munaya taji matuk'ar dad'i da ganin ashe harda y'ar uwarta a walimar, itama sunsha k'yau cikin Brown d'in kaya itada yaa Marwan, tana cikin less irinna Munaya, kalarce kawai ta banbanta, shikuma Yaa Marwan harda babar riga, maganar k'yawun dasukaima 6ata lokacine, suma Yaa Fadeel da Feena suna d'auke da yaransu. Sun shiga cikin hall d'in da tawagar rakkiyar Kuyangi da dogarai, masha ALLAH Munaya tafad'a dan ganin d'unbin jama'a da aka Tara a wannan k'aton hall, manyan mutane da iyalansu sun halarci wannan waje, hakama ahalinsu Munaya kwai da kwarkwata sunzo, harda y'an anguwarsu, duk yawan mutanen nan bai hana a saka mata kan tsaro masu tauriba a wajen. Kowa saida su Galadima suka birgesa, abin akwai tsantsar birgewa da sha'a a cikinsa, A cikin fans harda masu k'yasa Galadima🙆🏽. barama namuku gulma, can Na hango muku tawan Miss xoxo fa idonta kamar zai fad'o, hakama zee bawa da Aysha dansabo da kdeey🤥, dukda harar da Maman Khady da takwara billy galadanci ke musu sunk'i rusunar da idanu, lamari ya girmama Slimzy harda k'ok'arin mik'ewa fa wai zata iya barin sadeeq d'inta, da sauri saffiya Huguma ta maidata mazaunin tana hararta, Ummi Ai'sha tace, “kai dan ALLAH Ku nutsu kar'ace 'yan Haske muncika ruwan ido”, Faxy Fation da party zarah da Feedohm sukace ai Galadima d'inne fa yaji gishiri da magi, Hafsat Rano ta toshe baki tana dariya, hajja kam yitai kamar bata wajen, sai loda nama take a baki, Ayusher da khaleesat dake kallonta sukace wai hajja bazaki rage filiba a cikinki?, Mamu gee tace, “kukuma ga sa ido” “kema k'ya fad'a dai” cewar zee yabour, Asmy b Aliyu datun d'an tai shiru itada Ummu Basheer suka yamutsa fuska suna fad'in “please kuja aji mana 'yan haske, kunafa ganin yanda aka karrama mu fiye da kowa, karku jafa a maidamu kujerar baya wlhy”. Ni bilyn Abdull da lamarinsu ya girmeni nace, “kubarsu kudai kawai, sosuke susa a hanamu ganin sarakuna, kokuma mama Fulani ta rainamu, kuna dai ganin innaro ma kanta yanda taja aji ta kwamushe a gefe tana mazurai. Miss xoxo dake gefena tayi k'asa da murya tana dai-daita kanta, tace, “gaskiya kika fad'a tawan, nidai kinsan dama dai Galadima ya dad'e a k'ok'on raina, ko sau d'ayane kisan yanda kikayi aka mana hoto tare”. Nace, “karki damu tawan, Salfe ma zakuyi, amma fa ki kula, dan Munaya babu sauk'i”. “gulmar mi kukeyi?” cewar Ayusher tana jeho mana handkerchief d'in hannunta. zamanmu muka gyara nuna wani basarwa🥺, kunsan fa muma mun fara koya a wajen Galadima😜. Lallai, fans sannunkufa, lallai kunma munubiya da Munaya kara, ko Galadima nasan kun gama birgesa aradu, irin wannan anko da kukasha, ko a UK albarka y'ay'an baba buhari😝. ____________________ Isowar Sarki Jalaluddeen da Sarki Abdul-fatah da tawagar wasu amintattun sarakunan abokan Abie ya saka kowa ya mik'e cikin girmamawa, saida suka zauna sannan kowa ya koma ya zauna, an fara bud'e taro da addu'oi ga jarirai da kuma kakansu sannan aka fara gudanar da abinda ya Tara jama'a cikin nutsuwa. Kusan dai lamari Na manya, mudai Fans d'in raina kama sai zuba salfe muke, karkaje kabada labari ace k'arya ka zula bakajeba😆, shiyyasa muka kafa hujja koya kukace my sweet fans🤷🏻‍♀😂?. Masu 6oyayyen shiri a zuciyaa fa sunata k'iyasata yanda abubuwan da suka shirya zasu gudana, saidai kuma idan sunsan wata basusan wataba, dan eyeglasses d'in idon Galadima Google ne😏, (wato camera ne) tundaga Inda yake yanayo zooming d'in wad'anda suka k'arshen hall d'in ma, duk Wanda zuciyarsa ta saka masa alamar tambaya akansa yana tantancesu ne d'aya bayan d'aya. Nidai Galadima ka kula banda fans d'in raina kama😨🙆🏽. Anyi nisa da taro harma Anfara zubama cikin maik'o da mask'i, ga mai zak'i da sanyi muna korawa, Galadima ya kalli agogon azurfa dake hannunsa sannan ya d'ago ya kalli Muftahu suka had'a ido, lips ya ciza, Muftahu daya fahimci yaren ya gyad'a masa kai, ya kuma kallon Saleem da Nuren da Aunty mimi Mom and Sauban Samha Ayusher, kowannensu Kansa ya gyad'a alamar fahimta.................✍🏻 Turk'ashi, tofa masu karatu, shin mike shirin faruwane haka? Wannan amsa tana page 26 da zaizo ranar Monday insha ALLAH. musha weekend lafiya sisters and brothers.🙋🏻🙋🏻🙋🏻 Barkanku da juma'at😁🤝🏻 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ___________________ _Writer's namu ina mik'o gaisuwa da babbar murya_.🙋🏻 *_(takwara) Bily s Fari, (mamana) Maryam IG, (mamana) Ummu hanan, Hauwa'u A Usman (jidda😘) Rufaida Umor, Qurratul ayn, Ai'sha Alto, Leemat, gwoggo😜 Asykhaleel, miss Xakss, Jameela Janaf, (takwara) Ummie Garkuwa, Khadeeja Candy, Billy Sarki, Sister Naja'atu, Reefat yahya, Sad-Naf, Maryam wasagu, Maman Shaheed, classic Feedo, Mzzdady._* 🙆🏽 _Yawane da kufa. Alkairin ALLAH ya kai gareku aduk inda kuke, bilyn Abdull na nayinku wujiga-wujiga🥰😘😘👍🏻_ ___________________ ~Book 2~ 👉🏻2⃣6⃣ ...................MC yafara shelanta cewa wannan bikin sunafa an had'ashi da bikin birthdays ne, domin ranar haihuwar yaran tai dai-dai da ranar haihuwar iyayensu, dan haka suka had'e wannan biki a yau guri d'aya, dan a waccan ranar murnar haihuwar bata basu damar yanka cake ba😂. Dariya aka sanya, saboda a yanayin barkwanci mc yayi maganar, Galadima kam ai kod'an murmushin ma baiyiba, garama Yaa marwan ya murmusa. Galadima ya kalli munaya, cikin maganar nan tasa mai kamada an masa tilas yace, “Kina da sa'a”. “Sa'a kuma?”. ‘Munaya ta fad'a cikin yanayin mamaki’. Harya bud'e baki zaiyi magana sai kuma ya basar. ganin haka itama Munaya saita sharesa, dan takula yau y'an mulkin ne a kansa. Saida ya gama shan k'amshinsa sannan yace, “wannan ne karon farko da Sameer yata6a bikin birthday”. Baki munaya ta d'an ta6e, tana fad'in “Humm, kodai y'ay'anka suna da sa'a?, domin dai a dalilin haihuwarsu ne kayi”. “ko kina jealous ne?”. ‘yay maganar cikeda basarwa’. tura baki tai gaba. Idonsa akan yaransa yace “idan kika bari na kama wannan bakin a wajennan humm.” ya cije lips d'insa. Sanin k'aramin aikinsane ya akaita abinda ya fad'a d'in ya sata saurin gyara bakinta , tad'an saci kallonsa, ya wani Fiske tamkar ba shine yay maganar ba ma. ita dai tana mamakin kasaita da izza irinna bawan ALLAH n nan, jinin mulki yana da matuk'ar k'arfi a jikinsa. tunaninta ya katse lokacin da hankalinta ya koma kan abinda ke faruwa a hall d'in Khaleel da Aiyaan, Aryaan ne suka turo cake mai k'yau da tsari, Wanda yasha kwalliyar White and Golden, an saka sunan Galadima da shekarunsa 31years a sama, a jikinsa kuma daga can k'asa ansa Muhammad Sameer (Dadyn Triples), an d'ora candlestick🕯guda uku, Sai hotonsa da yay k'yau sosai cikin shigar sarauta. Galadima ya kalli Sauban da Samha, yasan dai wannan aikinsu ne, k'in kallonsa sukayi sukam ballema suyi gamo da tsarabar harara😅. Ita Munaya ma sai yanzu taga Su Aiyaan, batayi zaton anzo da suba, tunda bataga yaran gidansu k'anana ba a waje, sai manya maza da matan Na ma'auri. MC ya taso k'eyar su Khaleel har inda su Galadima suke zaune, kowanne aka d'ora masa yaro d'aya, suma mik'ewa sukayi bisa umarnin MC d'in, a tare suke takawa ita da shi, sai k'yastu ake zuba musu, masuyi a waya da masu cameras, sai gidajen TVs d'in da aka gayyata suna nuna live. Sun Isa gaban cake d'in hannunsa rik'e da sandarsa, kaikace sarkine da kansa (gaskiyar Munaya Galadima akwai k'asaita, Kodai sarkin da Kansa ya shafa masa lafiya🤭). Bayan anmasa wak'ar happy birthday yayma munaya nuni waita hura candles d'in. Cikin k'asa da murya tace, “yalla6ai bafa haka akeyiba, ka hura abinka da kanka”. Hannunta ya kama ya matsa yanda zataji zafi, yace, “zakiyi?”. Ai baima kai k'arshen maganarba ta risina ta hure wutar, hall d'in ya d'auki tafi. cake d'inma dan rigima wai saidai su yanka tare. “haba yalla6ai, saikace Na wani aure?”. Cikin ta6e Baku yace, “wama ya sani kona auren ne”. Shiru tayi bata tanka ba, dan itadai fatanta a rabu lafiya, hannunta ta d'ora kan nasa dake rik'e da wuk'ar suka yanka taren. nanma dai tafin akayi. Ya lakata a d'an yatsa ya duk'o gasu Aiyaan ya daddan gwalama yaransa a hanci da kumatu, sannan ya juyo ga Munaya da haushi ya kamata, ai ita yakamata ma yafara sawa ba yaranba. Itama akan hanci ya shafa mata yana fad'in “yalla6iya haushi kikajine?”. Kafin tabashi amsa yakuma lakata ya shafama Aryaan Khaleel da Aiyaan suma. Dole munaya ta had'iye maganarta. Amma ta kudiri saita rama. Itama itada Munubiya k'aton cake nasu aka kawo kalar pink and White , Munu da Yaa marwan suka taso a tare. Munaya da Munubiya suka rungume juna suna maijin dad'in tunawa da ranar haihuwar su, shekaru 20 cif da kwana 7. Sun yanka cake atare suka sakama juna abaki kad'an-kad'an, sannan kowacce cikin son tsokana ta lakatama y'ar uwarta a fuska suka rungume juna suna dariya da k'ananun hawaye, suncika shekaru 20 ranarda yaransu sukazo duniya suma. Abin ya birge mutane, Munubiya ta matsa ga mijinta ta saka masa a baki kad'an, cikin murmushi yace, “happy birthday my heartbeat ”. Tace, “Thanks you my luv” k'arasawa tayi ta sakama yaran munaya dasu Aryaan a kumatu, sannan ta sakama nata yaran. Munaya danta rama abinda Galadima yamata, takai cake bakinsa kamar zata bashi, saida ya bud'e baki saita juya ta shafama yaran Munubiya a kumatu, sannan nata. Yanda Galadima yay shock akan abinda Munaya tamasa sai mutane suka sanya dariya suna tafa mata, mai martaba da papi ma dai saida suka Murmusa. Munaya ta dawo ta dangwalama Galadima akan hanci tana masa gwalo. Shi kansa baisan k'asaitaccen murmushin ya kufce masaba, ya saka handkerchief ya goge yana dawowa mazauninsu ya zauna. Daga nan aka fara gudanar da wasa, Comedian's sukazo sukad'an saka mutane dariya, saikuma mawak'a da suka bada nasu salon. Tun da Galadima ya fara yawaita kallon agogon hannunsa su Muftahu duk suka sake shiri, dan lokaci yana gab kenan. Galadima yay k'asa da murya batareda ya kalli Munaya ba, yace “ki shirya, shirinsu na farko d'aukewar wutar hotel d'in nan gaba d'aya, na gaba kuma shine banida tabbas. Yara dai ALLAH yana tare dasu, gakuma su Aryaan suma”.. Cikeda mamaki Munaya ta kallesa, sannan ta kalli yaran dake gabansu a wani d'an gado mai k'yau. Jikinta har rawa yake tace, “yalla6ai mi su Aryaan zasu iya? Please k.....”. Hannu ya d'aga mata alamar karfa ta ishesa yace, “wani ilimin aduhuwar daji kawai ake laluboshi, kinsan kuwa dolene a gamu da had'arurruka Aciki”. batada za6i sainyin shiru, ta kalli su Khaleel daketa wasa da abinci a teble da suke zaune hankalinsu kwance. Hawayene ya cika mata idanu, yama za'ayi wad'an can sakarkarun yaran ace suna masu bama yaranta kariya? Yaushe suka gama sanin ciwon Kansu ma balle na waninsu? gaskiya wannan gangancine kawai, tasa handkerchief ta share hawayen da ke k'ok'arin zubo mata. Duk abinda take Galadima yana kallonta. duk tausayinta saiya kamashi, ya tuna da wahalar datasha, amma bashida za6in daya wuce hakan, kuma itace tabashi k'arfin gwiwa ai, yasaka aransa ko salwanta yaransa sukayi zaiyi tawakkali insha ALLAH. Duk Wanda yake cikin shirinsu Galadima ya gama shirinsa, haka suma mak'iya masu buri a shirye suke. Gaba d'aya saura mintuna 25 atashi, saboda gabatowar sallar magrib, a kuma time d'inne Sarki Abdul-fatah da Sarki jalalludden dadai duk wani babba Wanda sukazo tare suka mik'e domin tafiya, ganin haka Galadima yama Yaa marwan sigina da ido akan ya fita da Ameen and Ameena suma, yabi tawagar su papi, dan baya buk'atar a cuta musu.. Jikin Yaa marwan a sanyaye ya d'auki yaran ya fita cikin dabara, yana kallon y'an uku, shidai dan kawai Galadima ya dagene, amma bai kamata a saka yarannan a matsayin tarko ba. Munaya ma dai ta danne zuciyarta tayi shiru, tanason bama Galadima kwarin gwiwa. Su papi na fita y'an rawar k'oroso suka fara wasa, mintuna goma da aka basu ya k'are, sai wani mawak'i ya fara nashi, nanfa y'an mata da samari aka samu nayi, dama ganin su mai martaba ne ya sakasu nok'ewa, ana tsaka da cashewa hall d'in yay d'iff, wuta ta d'auke agaba d'aya hotel d'in, mutane aka fara hayaniya kowa na k'ok'arin damk'e dukiyarsa a hannu da k'ok'arin kunna fitulun waya. Gaba d'aya jikin Munaya yahau 6ari, ta fashe da kuka tana laluben gadon da yaran suke, ruk'ota Galadima yay yasaka a jikinsa, muryarsa na rawa yace, “please ki nutsu”. “bazan iyaba yalla6ai, karsu......”. Yay saurin rufe mata baki, da tattausan tafin hannunsa..... A dai-dai wannan lokacinne kuma wutar hotel d'in tadawo. Hall d'in ya kuma kaurewa da hayaniya, zaram Munaya da Munubiya suka nufi gadon da yaran suke ciki, wayam babu komai. Munaya tayi luuu zata fad'i, saurin ruk'ota Munubiya tayi, Galadima yataso daga inda yake shima zuwa garesu. hall d'in yagama rikicewa da tsantsar hayaniyar rashin ganin yaran, sai kallon kallo akeyi. Securitys d'in da aka baza sun rikice da wannan tashin hankali, dan sune mutane na farko da za'a fara tuhuma. Rufe hotel d'in akayi aka hana kowa shiga balle fita, Galadima ya shafama Munaya ruwa ta kawo numfashi, fashewa tayi da sabon kuka ta fad'a jikinsa, hannu biyu ya saka ya rungume ta shima yana had'iye kwallar bak'in cikin dake Neman zuboma idonsa. Tausayinsu ya kama mutane da yawa, innaro harda kukanta, hakama inno, abinda yabani mamaki shine tsantsar damuwar da mama Fulani ta nuna, dan itacema tabama Galadima ruwa ya shafama Munaya ta farfad'o. Da farko Munaya ta d'auka ko Galadima wasa yake mata yasan inda yaran suke, amma ganin damuwar da yake ciki saita kuma rikicewa, dandanan numfashinta yafara gagarar k'irjinta, ta mik'e a kid'ime, dan taji a jikinta kuka sukeyi, nononta sai tsitstsirawa suke, wani jirine yafara hajijiya da ita da zuciyarta ta k'iyasta mata zafa su iya kashe mata yara, luuuu tayi baya Galadima ya ruk'ota. sume musu ta kumayi. Hankalin Galadima kuma tashi yayi, dole ya d'auki Munaya aka sakata a mota suka bar hotel d'in. Sauran mutane kam kowacce mota zata fita sai an binciketa. Yayinda Securitys d'in suka bazu ko ina na hotel d'in ana bincikawa. Gida aka wuce da munaya, har suka isa tana jikin Galadima, yanata murza tafin hannunta kozata farfad'o, har d'ora bakinsa yayi akan nata ya jawo iskar numfashinta amma a banza, hakanne yakuma tada hankalinsa. Kai tsaye d'akinsa ya wuce da ita, ya shimfid'eta a kan gadon ya cire mata alk'yabbar jikinta, Akash suka k'araso da hanzari shima, taimakon gaggawa yafara bata shida doctor jalal, cikin amincin ubangiji saigashi takawo numfashi, bama su bari tadawo dai-dai ba suka mata allurar barci. Suna fita Galadima ya cire rawani da alk'yabbar jikinsa shima, ya sassauta bottom d'in wuyan rigarsa. Safa da marwa ya shigayi a tsakar d'akin yana Mirza agogon hannunsa Wanda daka gani kasan ba normal agogo bane,. Wayarsa datai k'ara yay saurin d'auka, d'agawa yayi yasaka a kunne, “Muftahu ya ake ciki?”. Cikin hakki Muftahu yace, “komai yana tafiya yanda ya kamata ranka ya dad'e, har yanzu gamu muna bin bayansu, amma munkai inda yakamata ka fara Controlling namu, yanzu mun.......” Da sauri Galadima ya katseshi ta hanyar fad'in “karka damu ina kallon Ku, saidai kilometer's d'in dake tsakaninku dasu fa yakai 1½, Saleem da Sauban sunfi kusa dasu, dan haka ku k'ara azama. daga lokacin da suka farga da abinda nasaka jikin Amaturrahman tabbas zasu cireshi, kuma zamu rasasune gaba d'aya”. “Ok babu damuwa, ranka ya dad'e”. Yanke wayar sukayi, Galadima ya bud'e wani k'aramin akwati ya fiddo kayan aiki wanda a ready dama yagama had'a komai, bajesu yayi akan gadon kusada Munaya, ya zauna yafara Control cikin matuk'ar kwarewa. Saleem ya kira aunty Salamah wadda itama take tare dasu Ameer yaran da suka sace Muftahu, d'agawa tayi jikinta na rawa, “Saleem kuna inane?”. “Aunty Salamah gamunan bayansu kad'an, amma mund'an basu k'afa saboda na kula sunfara fuskantar muna bin su, yanzu dai haka mun ajiye motarmu mun samu mashin”. “Hakan yayi, insha ALLAH indai ta Anguwar da muke tsammanin zasu shigane kamar yanda kaji Harun d'in yay magana to tabbas mu dai mun iso, saidai suzo su iskemu, ka kira yalla6ai ka sanar masa yakamata ya fito yanzu”. “no Aunty Salamah, bazai yuwu boss yabaro masarauta ba yanzu, saiya tabbatar mun Isa, saboda dukma inda suka shiga yana bibiyarsu, dan bazai saka yaransa a matsayin tarko ba babu tsaro k.......” Tai saurin k'atseshi ta hanyar fad'in “yauwa ina zargin kamar gasunan a wata bak'ar mota sun wicemu fa”. “Alhmdllh, su Ameer Susan yanda zasuyi su bisu bara na kira boss”. “ok”. Kawai Aunty Salamah ta fad'a ta yanke wayar. Kiran Galadima Saleem yayi, bugu biyu ya d'auka, “Saleem mike faru yanzu?”. “Ranka ya dad'e gamu dai biye dasu, amma Aunty Salamah tacemin gasu tagansu”. “wacece Salamah? ”. Gaban Saleem ya fad'i, dan ya manta Galadima baisan Salamah ba, “Am sorry sir, idan komai ya dai-daita zan maka bayani”. “Saleem!!!”. Galadima ya kirayeshi a tsawace. Saida Saleem ya janye wayar akunnensa, muryarsa na rawa yace “ka yarda dani sir, wlhy itama ta kwarai ce”. Ajiyar zuciya Galadima yayi, muryarshi cikin tsantsar damuwar yace, “wannan anguwar da kuke tanada hanyoyi da yawa, dan haka Ku fara amfani da live GPS navigation maps naku, yanzu zanyi settings komai yanda zaku ringa ganinsu duk layin da zasu shiga insha ALLAH, waye yake driving d'in a cikinku?”. “nine sir”. “ok bama Sauban wayar”. Saleem ya mik'ama Sauban wayar, Galadima na fad'a masa yanda zaiyi, shikuma yana Controlling maps App d'in dake cikin System d'in cikin kwarewa, (dan shima Galadima bai barsa hakaba, dukda bashida ra'ayin karantar wannan fannin saida ya tsaya tsayin daka ya koyan saboda irin wannan ranar). Saida Galadima ya tabbatar komai ya dai-daita, sannan ya kira su Nuren ma, suma suka dai-daita komai nasu, cikin sauk'i duk suka koma ganin inda yaran suke, saboda Galadima ya saka Abu jikin Amaturrahman, dukda bawai hotonsu ko video suke kalloba kai tsaye. Duk da haka Galadima ke fad'a musu su shiga layin haggu, ko dama, kosu canja hanya dadai sauransu. Duk Wanda yake a wannan masarauta yau hankalinsa a matuk'ar tashe yake, saifa kallon kallo da hasashen juna ake a zuciya, kowa yana zargin Wanda ya raina. Hankalin Abie a matuk'ar tashe ya nemi ganin Galadima, koda sarkin k'ofa yazo yana knocking Galadima bai amsaba, kuma yana kallonsa ta CCTV. d'an aike ya koma ya sanar Galadima ya kulle kansa a d'aki yak'i bud'e k'ofa. Papi inno ya kira, yace maza taje sashen Galadima taga mike faruwa. Ko kuyangi inno batajira sun mata rakkiyaba, hasalima babu Wanda yaga fitowarta a sashen mama Fulani, dan kowa a rikice yake da wannam bak'on lamari na satar yara. Galadima daya ga sarkin k'ofa yabar wajen ya mik'e shima daga gaban kayayyakin da yake aikin, shaddar jikinsa ya cire yasaka bak'in wando da t-shirt, ya kawo bak'ar jacket mai k'yalli kamar rigar sanyi ya ajiye gefe, a bakin gadon ya zauna yana d'aura takalminsa yana cigaba damasu Sauban da Nuren bayanin hanya, a dai-dai lokacinne Inno ta iso sashen nasa, da hanzari Sarkin k'ofa ya bud'e mata k'ofar, bata jira wani isoba ko masa sallama ta turo k'ofar falonsa ta shigo, babu kowa a falon, komai ma a kashe yake. Bedroom d'insa ta nufa, nandai saida tayi knocking kam, saidai kafin yay yunk'urin tasowa ya bud'e mata ta turo k'ofar ta shigo, mik'ewa yay yana kallonta da d'aukar jacket d'insa zai saka. Ajiyar zuciya inno ta sauke, saboda ganinsa normal. “Ranki ya dad'e da kanki? lafiya dai ko?”. “Inafa lafiya Muhammad? takawa ya aiko a kiraka ance ka kulle kanka, gashi baka sanar mana halinda yarinyar nan take cikiba”. Galadima yace, ba kulle kaina nayiba, bansan kuma d'an aiken daga papi yakeba” ya juya yana kallon Munaya da cigaba da fad'in, “itama ta farfad'o, amma sun mata allurar barci”. ‘ya k'are maganar da daidaita zaman kwalar rigar jacket d'insa’. Ajiyar zuciya inno ta kuma saukewa, tace, “to Alhmdllh. ina kuma zaka naga kana shiri?”. Wani murmushin takaici yayi zuciyarsa dake gudun daya wuce kima da suya ya dafe, Inno dai ta zuba masa ido, takowa yay inda take ya kama hannunta ya rankwafo (dan yafita tsaho) ya d'ora bisa kansa, cikin murya mai nuna tsananin karsashi da alwashi yace, “kisamin albarka inno, zanje farautane”. Da sauri ta janye hannunta daga kansa tana matsawa baya, “Muhammad mikake nufine? kana ganin tashin hankalin da muke ciki shine zaka k'irk'iro mana wani kuma? kana tunanin wad'annan mutanen zasu barkane? dama kai suke fako, shiyyasa sukayi tarko da bayin ALLAHn dabasu ji ba basu gani ba, su takawa cikin k'ok'arin d'aukar mataki suke, yanzu haka naga IG da kansa gashican ya iso bisa umarnin kiransu”. Galadima dake tattara abinda zai amfani dashi yana zubawa a aljihu, yace, “inno Muhammad Sameer d'inku ba ragon namiji bane da zai zauna jiran Police d'in da suka gaza gano wad'anda suka durk'usar masa da mahaifi tsawon shekaru a yanzu kuma nayi tunanin zasu iya dawomin da gudan jinina har uku, ba sune sukamin tarko ba nine namusu tarko, idan tsoron na mutu kuke, Ku cire inno, ko babusu mutuwa tabbataccen abune rubutacce a kundina, kimin addu'a saina saina dawo”.. Biyosa inno tayi har babban falo tana Kiransa amma yak'i dakatawa, saima d'aga mata hannu da yakeyi, yana gab da zai fita ya juyo yana fad'in “karki d'aga murya da yawa ranki ya dad'e, dan kunnen magauta a bud'e yake”. Yana fitowa Sarkin mota ya taso, dan suna zaune jigum-jigum a rumfar bunun dake sashen na Galadima, duk gaisuwar da suke masa babu ta wacce ya amsa, yau kam ko d'aga hannun basu samuba ma. Basu damuba dan dolene kowa yamasa uziri. Da kansa ya bud'e mota ya shiga mazaunin driver, Sarkin mota daya k'araso yace, “ranka ya dad'e ka gafarceni gani”. Da hannu yamasa nuni da gefen mai zaman banza batareda yace uffan ba. Sarkin mota bashida za6in daya wuce zagayowa ya shiga. A 360 Galadima ya ja motar, kamarma ya manta yana cikin masarautane, saida suka fito gaba d'aya sannan ya bud'e baki da k'yar yace, “ka dinga kallon bayanmu, dan nasan dole za'a samu masu binmu”. Da “to” sarkin mota ya amsa cike da girmamawa. Sarkin mota yace, “tabbas ranka ya dad'e ana binmu”. Cije lips Galadima yayi, ya canja hanya, cikin salon iya taku suka 6acema su Harun dake bin su tundaga masarauta. Hankalin Harun ya tashi kwarai da gaske, dan bai shirya fito na fito da Galadima ba yanzu, saiya cimma burinsa, daga nan komai ta fanjama fanjam, iya zagaye-zagayensu baiga ko motar datai kama data Galadima ba. Shima yana 6ace musu ya dawo kan titi sosai, Maps d'in GPS ne yazama jagoran Nuna masa hanya, da taimakon Sarkin mota kuma dayasan gari. Danshi Galadima ba tuk'i yakeba idan yazo 9ja, saidai idan ta kama tilas babu yanda zaiyi kamar irin haka. Sunyi tafiya mai tsawo, yayinda yake Communication dasu Nuren dasu Saleem. A haka ya iso inda suke, duk fitowa sukayi daga motocin, shima Galadima ya fito, idonsa akan agogon hannunsa, yad'an kallesu sannan ya koma kan waya yana fad'in, “maps d'in ya nuna suna a wajennan, kunga kenan tsakanin gidajennan guda hud'une dake kallon juna?”. “kwarai da gaske suna nan”. cewar Muftahu yana furzar da iska. Galadima yace, “Sauban da Saleem zaku cigaba da Control namu”. ‘yay maganar yana ciro agogon hannunsa ya mik'a musu, “ga wannan kuci gaba da using dashi”. Suka amsa da “to” suna kar6a. ya mak'ala abinda zai taimaka masa yaji magana, suma su Nuren duk yabasu suka saka. Har zasu bar wajen ya dakatar dasu ta hanyar d'aga musu hannu, takawa yay gaban k'ofar gidan farko ya haska gaban gate d'in da fitilar wayarsa, babu abinda yake nema, ya matsa na biyu ma haka, komawa yay d'ayan 6angaren, yana haskawa saiga sawun tayar mota data shiga gidan, duk'awa yay ya d'iba k'asar wajen ya shinshina, ya d'ago ido ya kalli gidan yana jizar lips, saiya zubar da k'asar daya d'iba ya mik'e, da hannu yayma Nuren da Muftahu nuni nan ne. Tahowa sukai garesa, Aunty Salamah datun d'azun suna daga cikin mota suna kallonsu suma suka fito ita da su Ameer. A tare suka rissina suna gaida Galadima ya amsa yana bin su da kallon mamaki. Da yake su Saleem sun sanar dasu Muftahu su Aunty Salamah d'in sai Nuren ya kuma yima Galadima bayani. Aunty Salamah tace, “ka gafarcemu ranka ya dad'e, nasan zakayi mamkin mun shigo abinda ba'a gayyacemu ba, insha ALLAH zakaji dalilin shigowar tamu nan gaba. game da shiga gidan nan mungama komai, maza 5 ne da mata biyu, wad'anda shigarsu ta tabbatar min suna cikin hadiman masarauta su matan kenan”. Kai kawai Galadima ya iya jinjina masa. daga nan yaymata nuni da zasu iya farawa. Da taimakon su Ameer suka shiga gidan. ★★*★★★*★★★*★★ Fitar Galadima da kusan awanni hud'u, around 2am Munaya ta farka a firgice, Inno dake zaune akan Sofa, mom da Aunty Mimi kuma a gefen gadon suka kalleta, tashi Mom tayi da sauri ta nufeta tana rik'eta, itama Aunty Mimi ta taso. Kuka munaya ta sanya tana fad'in “Mom sun mutu ko? Nasan dama kashesu zasuyi, Aunty Mimi dan ALLAH miye laifinsu su? kwanansu 7 fa kacal yau a duniya, mi suka sani game da abinda ake tuhumarsu? An durk'usar musu da kakansu, an hana mahaifinsu nutsuwar zuciya data rayuwa, shin wannan tabon bai Isa a barsu su taso da shiba a rayuwarsu? Har sai an had'a da salwantar dasu kenan?”. ta fashe da kuka maiban tausayi. Tasowa inno tayi ta zauna a bakin gadon itama, kamo hannun Munaya tayi ta kwantar da ita a jikinta tana shafa kanta, yayinda itama kwallar kebin nata kumatun. Aunty Mimi da mom ma duk hawayen sukeyi, kalaman Munaya sun ta6a zukatansu. Lallashinta da magana mai dad'i suka shiga fad'a mata, sai sauke ajiyar zuciya takeyi, ga jikinta yayi ringim da zazza6i saboda nononta sun mata hak'e-hak'e, rabonsu da shansa tunda rana, tausayinsu ya kuma kamata, tasan yunwa da k'ishi ma kawai sun Isa su k'arar da numfashinsu, hawaye masu d'umi suka kuma gangaro mata a kumatu suna sauka jikin inno dake shafa kanta. Shayi Aunty Mimi ta had'o mata, amma fir tace ta k'oshi, da k'yar inno ta samu ta lalla6ata tasha Quarter d'in kofin. Mom tace, “wannan nono kid'an matsesu kozasu rage miki nauyi, dan shine yakawo wannan zazza6in”. Bata musaba aka kawo k'aramin bowl ta matse aciki, Aunty Mimi ta zubar a bayi”.. Tanason tambayar ina Galadima tanajin kunya, sukuma babu Wanda ya sanar mata komai, kodan gudun k'ara tada hankalinta. Magani suka bata tasha takoma ta kwanta, yayinda sukuma suka mik'e duk suka d'aura Alwala suna mik'ama Ubangiji kukansu, danshi masanin sirrin 6oyene, yana kallon komai, kuma shine zai kawo iyakar komai d'in. ★★★★★★★ Duk wannan abun dake faruwa su Momma babu Wanda ya sanar musu, saidai sukaji a jikinsu tamkar akwai matsala, sunta kiran numbers amma daga wadda zasu samu a kashe sai wadda network zai hanata shiga. Sai suka d'aura ko shagalin sunan ne yakawo hakan. ******************* Tunda Munubiya suka koma gidan kuka takeyi, ko kad'an tak'i sauraren yaran da keta tsula kuka suma, balle tabasu nono. Ba itaba hatta su Ayusher dasu feena kukan sukeyi, hakama Samha harda shid'ewa, dan itama su tabi bata koma masarauta ba, Yaa marwan da mama Rabi'a ne kawai ke k'ok'arin danne nasu suna lallashinsu. Yayinda dare yay nisa duk sai suka d'aura alwala suka zo suna mik'ama Ubangijin talikai kukansu da k'ok'on barar bama wad'annan k'anan alhaki kariya da fatan ku6ta. A 6angaren gidan su Munaya kam duk hassadarsu yau dai sun tausayama gudan jininsu da yaranta, sundawo gidane kowa yana sharar kwalla da addu'ar ku6tar yaran. Ita innarsu Munaya ma ai ba'a magana, ALLAH kad'aine yasan halin datake ciki, ta shige d'aki ta rufe kanta tana jera nafilfili, dan wannance kawai gudunmawar dazata iya bayarwa a garesu akan wannan lamari mai sark'ak'iya da yawa. Abban su munaya ma yau harda hawayensa, dukda bashi da tabbas akan hasashensa yasan komai zasu iya, saboda SD yanada kusanci da wannan masarautar sosai, duk abinda ke hannunsa da bayanan daya ajiye ya shiga tattarasu waje d'aya...............✍🏻 😿Duk nisan jifa dai k'asa zai fad'o, kwana 99 na 6arawo, 1 kuma tak namai kaya.👎🏻 Fans insha ALLAH dai abuwa sun fara warwarar zare, sai mubi su Galadima muga yanda zasu dawo mana da triplets d'inmu gida😭, yau Munaya tabani tausayi daga ita har Galadima, dan shima dai dannewa kawai yake saboda jarumta, ALLAH ya rabamu da sharrin mak'iyi komai k'an k'antarsa, Harun da sauran munafukai MAZA BISA KANKU🏇🏻🏇🏻🏇🏻🏇🏻🏇🏻. Barkanmu da dawowa my sweet fans🤕😡. Yau bana cikin yanayin dariya😡 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣7⃣ ................Tunda suka d'akko yaran suketa kuka, musamman Abdurraheem dahar shid'ewa yakeyi, ALLAH dai yabasu sa'a ne saida suka fito suka fara kukan, neman haukatasu ma sukaso yi tun amotar, jisukai tamkar su rufesu da duka, saidai babu damar hakan, dan basuga abin duka jikin wad'annan kwad'unan yaranba. Da farko sunga kamar ana binsu, sai daga bisani ne sukaga ba haka baneba, har dai suka iso gidan y'an uku basu barsu sun shak'i iska ba. Suna shiga suka danna musu wasu allurai, cikin mintuna k'alilan jikinsu dukya saki sukayi luf. ganin lokaci yaja har kusan 10pm babu alamar wani motsi hankalinsu ya kwanta, dan sunsan dai tabbas sun tsira, wayar wadda ta sakasu aikin suka kira, amma tak'i yin picking. Cikin matan d'aya tace, “kusan dai bazata d'aga ba, saboda nasan masarauta a haukace take yanzu, saidai mubari zuwa safiya”. Tsaki d'aya yaja, “kai nifa gaskiya a tsorace nake, gara ta d'auka asan mafita, bana buk'atar gawar yarannan takwana a hannunmu, kunsanfa babansu mayene wlhy, tsaf zai bibiyemu”. “kai dalla ai yanzu bashida wannan damar, caza'ayi a fad'ama police, sukuma aikinsu zai farane zuwa safiya, kafin sannan munma gama binne gawar yaran mun kama gabanmu”..... “eh kumafa hakane”. Suna tsaka da wannan hirarne su Galadima suke shigowa, gidan k'aton gaskene dan haka suka kasa fahimtar INA zasu dosa, Galadima Yakuma danne abin kunnensa da d'anyatsa d'aya cikin murya k'asa-k'asa yake fad'in “Sauban kufara muje”. “yauwa Yaya zaku shiga hannunku Na haggu, duk sunajin maganar dan haka sukabi hannun haggu, yayinda su Ameer ke binsu a baya suma. Galadima dake gaba ya bud'e k'ofar a hankali duk suka shiga, daga can Saleem yace, “duk Ku rarrabu sir, dan abin ya nuna yaran suna ainahin tsakkiyar gidanne”. Batare da sunyi magana ba duk suka rarrabu. 'Daya acikin 6arayin yace, “kai nifa kamar motsi nakeji gaskiya”. “to sannu mai kunnen maciji”. cewar d'aya aciki. Cikin matan d'aya tayi dariya tana fad'in “nakula kaidai bibo matsoracine halan?”. Hannu ya d'aga zai kwad'eta, a harzuk'e yana fad'in “k wlhy kacaccalaki zanyi, bar ganin kinfito daga masarauta, kubadan ma an had'amu aiki dakuba kun Isa saninmu ne? jimin y'ar iskar mara kunya”. Hak'uri y'an uwansa suka bashi, ya mik'e yana jan tsaki ya fito danya duba. Galadima dake la6e cikin labule yay saurin fitowa, abinka da dogon mutum dan danan yasamu damar shak'osa ya shaka masa abin hannunsa, tun yana k'ok'arin kare kansa har jikinsa ya saki ya kwantar dashi a k'asa. Jinjina Muftahu dake kusa dashi yamasa, sannan suka cigaba da shiga. 'Dayar baiwar tana kitchen tare da wani suna iskancinsu Nuren yasamu damar sad'ad'awa, (kunsan dai shahararren kidnapper ne🤭😂) yauma tsiyar ya aikata wajen jefa ma namijin handkerchief a fuska, macen tai yunk'urin zuba ihu yasa k'afa ya tad'ota ta fad'in, sannan ya danne bakinta da ya shak'a mata itama. K'arar fad'uwarta taso fargar da sauran, dan haka duk suka mik'e suna fara lek'e-lek'e, aikam Muftahu yasamu ya tad'e d'aya ya fad'i, Ameer dake bayansa shima ya shak'a masa, harda mangareshi yana fad'in “kwallon shege taka ta k'are, inakai ina satar sarakunanmu insha ALLAH”. dariya taso kufcema Muftahu amma ya danne bakinsa da hannu yana girgiza kai saboda tsiyar Ameer. Fad'uwar wani da suka juyo ya sakasu kuma saurin waigawa wajen, Galadima ne ya sakeshi ya fad'i, “shegen k'arfin jinine dashi dak'yar abin yay masa tasiri”. Galadima ya fad'a yana halbinsa da k'afa. Gaban d'ayar baiwar dake la6e jikin labule ya fad'in, dan tabbas wannan muryar Galadima ce, kowa yasan bai iya R ba, zuface tashiga keto mata jikinta na 6ari, ta to she bakinta saboda kuka daya kufce mata, saigata tana tsilala fitsari saboda ganin Galadima yanufo ta wajen, shikenan itakuma tata tak'e, wannan zakin gagara badau d'in binneta kawai zaiyi da ranta. Waige-waige Galadima ya fara saboda jin numfashin mutum dayakeyi kad'an-kad'an ta wajen, har yayi gaba ya dawo baya yana yaye labulen wajen. shi da farkoma ya zata aljanace saboda yanda ta zazzaro masa ido. fincikota yayi ya Watso tsakar d'akin, mamaki ya kamashi ganinta da kayan manyan kuyangin gidansu. “tashi tsaye”. ya fad'a cikin matuk'ar d'aure fuska, kad'an yarage kashi ya kufcemata. “ina suke!!!”. Yafad'a cikin matuk'ar tsawa daya firgita hatta su Sauban dake saurarensu a waya. Wannan tsawar tasa ce ta saka d'ayan fitowa a tsorace da gun a hannu, Aunty Salamah dake bayansa bai saniba ta hankad'ashi yay gaba zai fad'in, Nuren ya ida tad'eshi da k'afa. Gun d'in data fad'i ta silalo gaban Galadima ya taketa da k'afa yana huci da taunar lips. Handkerchief d'in hannunsa yasaka ya d'auki bindigar, ya saita namijin da ita. Mazari jikinsa ya fara yana d'aga hannu sama, “dan ALLAH ranka ya dad'e karka kasheni, wlhy bansan komaiba, oganmu ne yasan komai da wannan baiwar”. Kunamar bindigar Galadima ya d'ana, nanfa su Muftahu duk suka rud'e, Nuren yace, “Brother please karkayi harbi, nasan zasu fad'a mana, dan ALLAH kayi hak'uri”. Gaba d'aya jijiyoyin kan Galadima sun mimmik'e, sai fidda huci yakeyi a wahalce. Muftahu ma yashiga rok'onsa, Su Saleem dake sauraren komai dagacan duk suka rud'e, Sauban yace “yaa Sam ALLAH ya huci zuciyarka, amma idan ka aikata haka a wajenwa Zamu samu hasken sauran abubuwan?, dan ALLAH kayi hak'uri badan mun isa mu saka ka ba, saidan halin da mahaifinmu ya tsinci Kansa tsawon shekaru, gakuma dama tazo mana ta Sanin sirrin 6oye, muyi amfani da ita ta sauk'ak'ak'iyar hanya....” Sakin gun d'in Galadima yayi ak'asa yana dafe k'irji, wani mugun bugawa zuciyarsa keyi, da baya-baya yanemi zubewa a k'asa, cikin hanzari Nuren da Muftahu suka taresa, da taimakonsu ya zauna akan kujera. Yana nuna baiwar da d'ayan hannusa. Aunty Salamah data fahimci mi yake nufi tace, “ina yaranne?”. Jikin baiwar Na 6ari ta nuna k'ofar wani d'aki, shiga Aunty salamah tayi itada Ameer suka d'akkosu. Saidai duk a firgice suke, dan yaran babu alamun rai tare dasu, zufa ta shiga ketoma Aunty Salamah, haka ta fito rungume da Abdurraheem da Amaturrahman, shikuma Ameer ya d'akko Abdurrahman yana fad'in “Aunty kamarfa yarannan sun mutu”. Wannan kalma caraf a kunnen Galadima. Wata muguwar zabura yayi yamik'e tsaye, sai ya kuma dafe k'irjinsa da sauri hajijiya tafara katantanwa dashi, basu fargaba sai jinsa sukayi kawai a k'asa. Gaba d'aya suka kuma rikicewa, sukayi kansa. Muftahu yace, “bamuda isashen lokaci, asuba ma ta gabato, dolene mubar gidannan dan ko yaushe zamu iya gamo da abinda bamu shirya masaba”. Duk sunyi na'am da wannan maganar tashi, nan fa suka fara kwasar wad'anda suka sumar suna kaiwa mota, sannan suka tasa k'eyar d'ayar baiwar da wancan, suma. Yayinda Nuren yad'an bincika gidan, ganin babu wani abunda zasu k'aru dashi yazo suka kama Galadima daya Suma suka fita dashi. Hankalin Sauban ya tashi matuk'ar tuk'ewa, ya fito yana nufarsu da ta6a jikin d'an uwansa, “Yaa Nuren miya farune? miya faru da Yaa Sam?”. “Sauban bamu hanya, ba lokacin wannan baneba yanzu”. Sole Sauban ya matsa baya hawaye Na kwarara a idonsa, suka shinfid'ar da Galadima a bayan mota, sai lokacin Sauban yaga yaran a hannun Aunty salamah da Ameer, da hanzari suma ya nufesu, Aunty salamah ta bashi Abdurraheem, jujjuya yaron yayi yaji kamar baya numfashi, “innalillahi....” yashiga maimaitawa zufa Na keto masa, dolene Yaa Sam ya suma, hawaye yafarayi yana rungume yaron a jikinsa, Tausayin dukkan ahalinsa da suka kwallafa rai ga yaran ya kamashi, musamman ma iyayensu, ya ALLAH nasan bazaka jarabcemu da abinda bazamu iyaba, ALLAH kabamu juriya”. Muftahu yace, “su shiga mota, duk shiga sukayi, Nuren dasu Ameer suka wuce da wad'ancan sauran wani waje daban, Muftahu kuma ya kira police d'in da suka shirya komai dasu, a hanya suka had'u, sai sukai joining d'insu tamkar tare sukayi aikin, suka kira manyansu suna sanar musu gashifa sun kama wani matashi da baiwar masarauta da yaran.... Wannan labari yama su d.p.o dad'i ya kira IG shima ya sanar masa, yaji dad'i shima, koba komai mai martaba zai yaba k'ok'arin dasukayi, akace yanzu suna inane?. Amsawa sukai da gasu a masarauta, dan harda Galadima sukayi aikin, yana kuma cikin wani yanayi shida yaran yanzu haka. Basuda za6in daya wuce suce musu to suma gasunan zuwa masarautar. Tun'a mota su Muftahu sun gargad'i baiwar nan da d'ayan mutumin akan suce su biyune suka sacesu, inhar sukace basu kad'ai bane wlhy saiya kashesu, sannan su tanaji fad'ar wani abun ba ainahin gaskiya ba, (dan Galadima baya buk'atar police su shiga cikin aikinsa yanzu, yafison saiya kama kowa sannan, dan inhar police suka shiga aikin mutane da yawa zasuyi escape ne) shiyyasa Muftahu yayma wad'ancan gargad'in tunma kan su k'arasa cikin masarauta. Da yawa wasu basu rintsaba a masarauta gagara badau yau. Munaya dai dole aka sake d'irka mata allurar barci mai k'arfi, dan kusan kuma haukace musu tayi gabannin asuba, dalilin wani barci daya figeta tayi mafarki mai matuk'ar tada hankali. Su inno Na zaune har yanzu suna kai kukansu ga ALLAH Muftahu da Sauban suka shigo d'auke da Galadima da suka kamo tamkar gawa, sai Saleem da police biyu dake falo d'auke da yaran sukuma. Zaram duk suka mik'e suna tambayar lafiya? Miya sami Galadiman?. Basu sami wata amsaba, saida suka kwantar dashi a gadon sannan Sauban ya share hawayen fuskarsa yana fad'in “suma yayi inno”. Aunty Mimi da mom sukayi kan Galadima suna kuka, inno tace, “kun samo yaranne?”. “eh gasu can a falo tareda police, saidaifa duk sun mutu, shiyyasa ma Yaa Sam ya suma”. yak'are maganar yana kuka. Hawaye suka zuboma inno, waya ta d'auka ta kira papi, Wanda shima dai a zaune suka kwana dagashi har Sarki jalaludden. A time d'in dama har ankai musu bayanin shigowar su Muftahu d'in. Yau dai kam tilas Manyan Sarakuna biyu suka nufo sashen Galadima da Kansu, abinda waninsu bai ta6a yiba kenan. Maganar ganin yara yafara baje Masarautar tun'a daren, dan kowa kunenensa a bud'e yake, da masu fatan a gansun da masu fatan kar'a gansun. Lokacinda papi da mai Martaban suka iso Inno Na rungume da yaran duka tana hawaye, sukuma su Aunty Mimi suna bedroom wajen Galadima. Kusan a tare Akash da Dr jalal suka iso dasu papi. Mai Martaban da papi suka kar6i yaran daga hannun inno, Suna zama bisa kujerun. Akash wajen Galadima ya nufa, dukda ba shine likitansa Na zuciya ba zai iya bashi taimakon gaggawa, shikuma Dr jalal ya fara kar6ar Abdurraheem dake hannun inno, yan d'ube-dube, yayi Na tsawon lokaci kafin ya ajiyeshi ya kar6i Na hannun mai Martaban, shima yagama duk abinda ya dace ya kar6i Amaturrahman a hannun papi, ajiyar zuciya ya sauke yana fad'in “Alhmdllh duk basu mutuba, allurar barci mai k'arfi sosai suka musu, shiyyasa numfashinsu yay nisa sosai, danta musu k'arfi da yawa, amma idan kuka saka kunne nawasu mintuna saitin jikin zuciyoyinsu zakuji suna motsawa kad'an-kad'an, sai dai ta wannan tafi yin k'asa sosai gaskiya”. Ya nuna Abdurraheem dake hannun inno. Su mai Martaban suka sauke ajiyar zuciya suna hamdala ga ubangiji. A cikima Akash nata iya bakin k'ok'arinsa ganin Galadima ya farfad'o, Ahaka su mai Martaban suka k'araso cikin d'akin d'auke da yaran a hannun, Munaya Na gefen Galadima an lullu6a mata bargo batasan wainar da ake toyawa ba, dan barcin nata shine mafita fiye da zama ido biyu. A gadon suma yaran duk aka shimfid'esu, Dr jalal yad'an musu dabarun likitoci sauran kuma aka barma ubangiji ikonsa Na jiran farkawarsu. Hankali kuma duk saiya koma ga Galadima da aketa fama. Har aka kirayi sallar Asubahi babu amo babu labari akan farfad'owar tasa. daga k'arshe dai Akash saida ya kira likitan Galadima na zuciya. Shiya dunga fad'ama Akash d'in yanda yadace yayi, lokacin shiga salla ya saka su mai Martaban fita masallaci dole, sukabar Akash da Dr jalal dake taimaka masa suna aikinsu, saisu Aunty Mimi da suka kasa matsawa ko nan da can, Sauban ma da k'yar su papi suka lalla6asa yabisu salla. Har gari ya waye sashen Galadima ya cika da manyan masarautar irinsu mama Fulani matan Sarki da sauransu Galadima babu wani bayani, zuwa yanzu ma wasu sun fara tunanin kodai yama mutu ana 6oyewane kawai. Wajen 8:00am Dr Yaseen Ali Modibbo babban likitan zuciya da akeji dashi ya iso, bisa kiran da Dr jalal ya masa yafad'a masa, dan abubuwan da sukaima Galadima bai farfad'oba Akash yakuma sanarma likitansa, shine yace tofa gaskiya Kodai asamo ainahin likitan zuciya ko kuma su taho dashi kafin cikar awanni 12, idan ba haka ba komai zai iya faruwa. A k'iyasin da sukayi cikin awanni 12 bazasu Isa india ba, tunda duk tsiya sai an samu jirgi mai tafiya, sannan ma kafin komai ya biyo baya. Hakkane yasaka Dr jalal kiran Dr Yaseen Ali Modibbo d'in, cikin amincin ALLAH kuma ya amsa zaizo d'in, saikuwa gashi ya iso. Canjama Galadima d'aki akayi, dukkan kayan aikin da Dr Yaseen yazo dasu aka shigo dasu, rufe d'akin sukayi suka duk'ufa su uku kansa suna taimakon Dr Yaseen d'in. Sun jigata kwarai da gaske kafin zuciyar Galadima tafara bugawa k'asa-k'asa, sai numfashinsa yafara fisga yana k'ok'arin fita. Duk ajiyar zuciya suka sauke. Suka cigaba da aikinsu, ana sakama Galadima wani abu a k'irji kamar dutsin guga, saiya girgiza sannan a cire, akuma maidawa. Basu barsa ba saida yasaki wata ajiyar zuciya mai matuk'ar sauti, harsu mai Martaban dake falo saida suka jiyosa kuwa. Wannan ne yasaka zukatan doctors d'in uku sanyaya, Dr Yaseen da Dr jalal suka had'a baki wajen fad'in “Alhamdulillah!”. Numfashin Galadima ya dawo dai-dai, amma sun masa allurar barci danya samu nutsuwa. Yaranma an kawosu ne Dr Yaseen ya kuma bincikawa, shima dai yace suna da ransu, amma Abdurraheem yanada ciwon zuciya shima, shiyyasa yafi sauran y'an uwansa jigata, ALLAH nema dai yay rabon yanada sauran numgashi, amma allurar tamasa k'arfin da zata iya dakatar da bugun zuciyarsa. Suma dai sun kuma samun taimako, musamman ma dai Abdurraheem da tausayinsa ya kama mutane da yawa a wajen. *_2:00pm_* Zuwa wannan lokacin Munubiya da mama Rabi'a da Ayusher Feena duk sunzo masarautar, Hakama baba k'arami da daddy, dan an sanar musu samo yaran da halin da galadima yake ciki. Amma saboda kara irinta Abba da innarsu Munaya sai suka bar su Baba k'arami da maman Fauziyya da mamansu yaa Hameed, maman Safara'u suka taho, sai innaro da gwaggo Safiyya. Ba'a barin wani bak'on fuska shigowa masarautar a yau, amma su sai mai Martaban yasa aka shigo dasu, basu samu ganin ko d'aya a cikin su Munaya ba, saidai Munubiya da aka shigar d'akin galadima inda Munaya ke kwance, Sauran kuma sun shiga ayarin y'an zaman jigum-jigum da jiran tsammani. Har zuwa wannan lokacin Galadima da Munaya babu Wanda ya farka, Amaturrahman da Abdurrahman dai sun farfad'o, sai dai suna kuka ko fita bayayi. Wanka laraba ta musu aka gasa musu jikinsu sosai, yau dai dole aka nemo madarar da Galadima bayason susha d'in, ita aka dama aka basu sukasha, aiko sun shata sosai dan yunwa sukeji, bayin ALLAH, rabonsu da abinci tun jiya da rana kusan I war haka d'in. Tausayinsu ya kama Munubiya dake basu madarar, tana yi tana sharar hawaye, da da farko nono inno tace ta basu, sai papi yace, “a'a kar ayi wannan gangancin, dan ba'asan abinda ALLAH zaiyiba wataran, ko akwai k'addarar aure a tsakanin yaransu, kar azo ayi Dana sani a watarar da baza'a iya maido wannan ranarba balle a gogo 6arnar da akayi”. Kowa ya gamsu da wannan magana, dan haka Muftahu yafita suka nemo madara shi da Saleem. Shine aka basu. Baiwar da aka kami da mutumin kuma suna hannun police, kuma kowa yaji cewar tana cikin bayin gidan wad'an da aka aminta dasuma sosai, saidai ba'asan ta wane sashe bace. Wannan Abu ya tsurar da zukatan Sauran bayin, dan dolene ya shafesu. Hankalin Uwargidan Sarki Sarauniya Zulfah (mahaifiyar su matawalle) a tashe yake, amma dayake ta iya takunta bazaka ta6a fahimtar haka ba, saima nuna tsantsar damuwarta akan lamarin da tayi fiye da sauran matan Sarki. dama kuma tafi nuna kulawarta ga Galadima kowa yasan wannan, shiyyasa babu Wanda yakawo wani Abu game da ita, saima wasu daban ake zargin. Munaya da Galadima sun farfad'o ne kusan time d'aya, amma Galadima ya riga Munaya, dama allurar awanni 4 kacal aka masa, da Sunan ALLAH a bakinsa ya farka, sannan yafara kiran yaransa d'aya bayan d'aya yana fad'in karsu tafi su barsa.. Rik'eshi Dr Yaseen yayi yana fad'in “ka kwantar da hankalinka ranka ya dad'e, dan zuciyarka tana cikin yanayin jiran k'iris ne, inamaka albishir da cewar yaranka suna raye, yanzu nan zakagansu insha ALLAH”.. Galadima ya sauke nannauyar ajiyar zuciya yana kallon Dr Yaseen, ya lumshe idonsa a hankali sannan ya bud'e, hanunsa ya d'ora akan saitin zuciyarsa saboda wajen yamasa matuk'ar nauyi. Ana haka Dr jalal ya shigo d'auke da yaran biyu, dan Abdurraheem shi yanan a d'akin kusa dashi bai farfad'o ba. Tunda Galadima yaga yaran sa suna a raye saiya kuma rungumesu a k'irjinsa da Dr jalal ya d'ora masa, wasu hawaye masu zafi suka gangara gefen kunnensa. Dr Yaseen yaji dad'in kukan da Galadima d'in yakeyi, dan zai rage masa rad'ad'in da yakeji da nauyin zuciyar, hakan ya nuna aikinsu zaiyi k'yau insha ALLAH. Galadima ya dad'e rungume da yaran, saidaga baya ya farga babu guda d'aya. A hankali ya bud'e baki yana fad'in, “ina d'ayan?”. Murmushi Dr Yaseen yayi, yace, “gashi a gefenka yana barci shima”. Juyawa Galadima yay ya kallesa, ganin d'an cikin yaron Na motsi alamar fitar numfaahi sai dad'i ya kuma ratsashi, ya lumshe idonsa yana yun k'urawa zai tashi zaune, taimaka masa. Dr Yaseen yayi, yatashi rik'e da yaransa, kwantar dasu yayi sannan ya matsa ga Abdurraheem hannunsa dafe da k'irjinsa har yanzu, rankwafawa yay kan yaron ya sumbaci goshinsa da kumatunsa, sannan ya shafa kansa la66ansa suna motsawa alamun yana masa addu'ar fatan samun lafiya a garesa shima. A 6angaren Munaya Itama tana farkawa da kuka ta farka, tana kiran yaranta, itadai afad'a mata idan sun mutu kawai saita hak'ura. Rungumeta Munubaya tayi tana lallashi da mata albishir d'in dawowar yaran garesu, hakan yasaka Munaya d'agowa da sauri tana kallon Munubiya, “Sweetheart da gaske kikeyi?”. “da gaske nakeyi Sweetheart, yanzu haka suna tare da mahaifinsu”. Dad'i ya ratsa Munaya, ta kuma k'ank'ame Munubiya suka rungume juna suna kuka da dariya lokaci d'aya. Hakan kuma saiya sanya su inno kukan tausayinsu da sha'awar wannan k'aunar juna nasu. Saboda su mai Martaban sun shiga wajen Galadima sai akace ita Munaya tayi wanka kozataji k'arfi kafin su fito. Bata musaba ta amince, ruwa mai zafi laraba ta had'a mata, tashiga wankan. Tanayi tana kukan farin ciki. bata cuci kantaba tayi wanka sosai ta gasa jikinta. Kafin ta fito an gyara d'akin tsaf, sai k'amshin daddad'an turaren d'aki yakeyi, babu kowa duk sun fice. Su mai Martaban suna tare da Galadima, sunyi farin cikin tashinsa, hakama yaran. sunkuma yima Abdurraheem addu'ar tashi shima. Sun d'an jima a d'akin, dan har saida aka shigo dasu Dady da baba k'arami, Yaa marwan, Yaa Hameed suma suka gaidashi da masa jajen ALLAH ya kiyaye gaba sannan suka fita gaba d'aya. Daga nan manyan irinsu mama Fulani, inno matana Sarki da sauran su duk suka shigo suma, harda su innaro da akaita kuka. Galadima dai Kansa kawai yake iya d'agawa, idonsa a lumshe. Baya buk'atar kallon kowa a cikinsu. Su inno duk tausayinsa ya kamasu. Innaro aka share hawaye tace, “barka da arzik'i kaji, ALLAH ya kiyaye gaba, ya shiga tsakanin nagari da mugu, ya tona asirin duk makirin dake cikin wannan satar yara”. Duk da amin suka amsa. Galadima ma yace amin akan la66ansa. sai tunani yake ina Munaya take?, dan hankalinsa yafara tashi da rashin gilmawarta, musamman daya tuna a halin daya tafi itama ya barta. Yadai kasa daurewa ya bud'e baki da k'yar yace, “Mom ina Munaya wai?”. Saida mom ta matso da kunnenta sannan tajishi, tasan yana lafiya ma ya aka k'are da k'asaitar magana balle yanzun. Murmushi tayi, tace, “tana d'aki, itama sai yanzu ta farka, dan dole aka sake mata allurar barci bayan tafiyarka, waccan bata dad'eba ta saketa”. Tausayin Munaya ya kuma kamashi, ya jinjina kai yana yunk'urawa zaune sosai. Cikin yamutse fuska yace, “Mom nima yakamata nayi wanka Na rama sallolin dake kaina”. Mom tace, “to bara a kira su Muftahu su kamaka ”. Kansa ya girgiza mata da mata alamar, zai iya da kansa. Mom tace, “Alhmdllh”. Rigarsa ya jawo yasaka, dan da dagashi sai best. d'aukar Abdurrahman da Amaturrahman yayi ya fito, yabar mom tana gadin Abduraheem dabai farko ba. babu kowa a falonsa Dan duk sun fice. Da k'afa ya turo k'ofar, Munaya Na zaune a bakin gadon rik'e da mansa zata shafa amma dukta kasa, burinta taga halinda Galadima da yaranta suke ciki kawaine damuwarta, gashi har yanzu babu Wanda yazo yakirata akan su papi sun fita. bud'e k'ofar ya sakani d'ago ido. Zummbur na mik'e tsaye ganin Galadima rungume da yaran, ai yau nama manta dawata kunyar towel na d'aura, hawaye suka shiga zarya tsakanin idona da kumatu, Galadima ya tako a hankali zuwa gareni idonsa a kaina. Da sauri namatso garesa nima, nahad'ashi shi da yaran na rungume ina sakin kuka mai k'aramin sauti. Shiru yay kawai ya zubama gashinta ido yana tausaya mata daga ita har yaran, ansakasu a yak'in dabasu San mafariba, ya godema ALLAH da yarannan sunada sauran numfashi a duniya. Da baisan yanda zaiyi da munaya ba. Ganin kukan nata zaiyi yawa ya bud'e baki da k'yar yace, “ya isa mana”. d'ago idanu nayi na kallesa, cikin muryarta data dishe saboda kuka nace, “Nagode yalla6ai, dasun mutu nima mutuwa zanyi”. Murmushin gefen baki yayi, cikin d'age gira d'aya yace, “dama ana sonmu haka?”. Sai yanzu kunya ta kamani, nai k'asa dakai ina kallon k'afafunmu. Bai sake cewa komaiba ya ra6a ta gefena yaje ya shimfid'e yaran akan gado. bathroom ya nufa yana cire rigar jikinsa, nidai Na k'arasa gadon Na rungume yaran ina sumbatarsu, wani dad'i da tsantsar farin ciki Na ratsani, Na d'aukesu Na fara shayar dasu ko zasu rage nauyin da sukamin, aikam kamar jira sukeyi suka kama sha. Hannun rigar namijin Na d'aga saboda tanan muke gane shaidarsu, ganin Abdurrahman ne saina fara tunanin ina Abdurraheem shikuma?, hankalina yaso tashi amma saina daure ina jiran Galadima ya fito naji daga garesa. Galadima dake kallonta bata saniba ya d'an cije lips, ya tabbatar yanzu tana son yaransa, amma baisan miyasa take ignoring d'insu ba idan yana waje? Kokuwa tsabar jan ajinne oho?. Har Lokacin daya fito wankan tana shayar dasu, ta shafa kan wannan ta shafa Na wannan, sosai suka birgeshi itada yaran, jin kamar motsi yasakani kallon wajen, da sauri na janye yaran daga bakin nono naja towel d'in na rufe abinna ina turo baki gaba. Baki ya ta6e yashiga takowa inda muke, ya rankwafo kaina ruwan fuskarsa yana d'iso min a jikina, a kasalance yace, “wane darene jemage bai ganiba malama, tunkan su sha ni........”. Da sauri na saka hannu na toshe masa baki. Zama yayi yana janye hannunna, cikin waro idanu yace, “to mikike tunanin zan fad'a? lallai kinfi k'arfina, niba can Na dosaba to”. Sosai naji kunya, na sauke yaran a kan gadon na sakko, zuciyata cikeda mamakin sa, ya d'aure fuska yana basarwa yayta sakin magana kuma kamar bashi yayiba. Ficewata nayi bayan na d'auki bathrobe d'insa na d'ora akan towel d'in jikinna. Wani kallo ya bita dashi yana ta6e baki, kafin ya maida ga yaransa daketa kalle-kalle, ya shafa kumatunsu sannan ya mik'e zuciyarsa na tunanin su Momma, addu'arsa d'aya kar wani ya sanar musu. Kasa fitar nayi saboda jin kamar da mutane a falon da zanbi ya sadani da 6angarena. Badan nasoba tilas Na dawo baya. Galadima dake gaban mirror yana shafa mai yana kallonta ta ciki, amma sai yayi biris tamkar bai gantan ba. Komawa nayi na zauna a bakin gado ina tunanin mafitar yanda zan samu kaya, da jin haushin sharenin da yayi. Ana haka mukaji knocking, saida ya kalli Computer d'in yaga Mom Ce d'auke da Abduraheem sannan ya mik'e yana amsawa.. Zuwa yay ya bud'e mata, bata shigoba ta mik'a masa yaron da har anmasa wanka Ashe, ta mik'a masa kaya a leda tace na Munaya ne. Galadima yace, “mom ya tashine?”. “ya tashi, tunma fitowarka babu dad'ewa, harma an masa wanka”. Sumbatar kumatun yaron yay yanama mom sannu Idonsa akan yaron yana kuma sumbatar goshinsa cikin lumshe idanu ya k'araso inda nake dana zuba musu idanu cikeda sha'awa. Kusa dani ya zauna ya d'ora minshi akan cinya. nima rungume kayana nayi na sumbaci goshinsa, inason bashi abinci amma inajin kunyar Galadima, gashi ya zubamin ido yak'i tashi. Lura da hakan dayay ya sakashi yin miskilin murmushi ya mik'e yabar wajen. d'an hararan bayansa nayi ina fad'in mugunta dai babu k'yau a kan la66ana..................✍🏻 “Hummm fans nasan kwace wai ina Harun ne?🤔, kumuje zuwa dai danjin ina ya shige haka? Ita kuma sarauniya Zulfah (uwar gidan Sarki mike matsalarta)?.😨😏 *_Ya Rabbi ka gafarta ma iyayenmu_*😭👏🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣8⃣ ............A yanda Na kula har yanzu bayajin dad'in jikinsa, dan komai a d'an wahalce yakeyinsa, koda ya fiddo kayan daga wardrobe saiya dawo bakin gadon ya zauna ya dafe Kansa, kallonsa nayi cikin damuwa nima, Na cire Abdurraheem Na kwantar, sannan Na mik'e zuwa garesa, durk'usawa nayi Na d'ora hannayena akan gwiwarsa, “yalla6ai lafiya?”. Shiru yamin kusan minti 1, harna fidda ran samun amsa ma na yunk'ura na mik'e da nufin barin masa d'akinma duka. Hannuna ya rik'o, na juyo na kallesa, har yanzu yana yanda yake baiko d'ago motsa ba. Na cije lips ina had'iye kukan dakeson zubomin, rayuwar nan tasa bana sonta wlhy, ni y'ar dangi Ce, nariga natashi gidan yawa, dukda gidanmu bahagon gidane mukanyi hira koyayane, amma shifa magana ma idan bai ra'ayiba wahala take masa, Abu na damunsa a rai amma bazai iya fiddashi yaji sauk'iba, Momma ta had'ani da aiki, a watannin baya kad'an kamar yafara canjawa, amma gashi yakuma birkicewa yanzu, tayaya Momma take tunanin zan iya canja Galadima? murd'ad'd'en mutumne shi mai wahalar sha'ani, ga tsantsar mulki da k'asaita da suka zama jinin jikinsa, s......... Tunanina ya katse lokacin danaji an jawoni, nai firgigit saboda fad'awa danayi jikinsa, shikuma yay baya ya fad'a kan gadon, kad'an ya rage mu danne Amaturrahman, yad'an kauce kad'an yana sauke ajiyar zuciya. Uffan bai ceminba ya maida idonsa ya lumshe. Mamakin wannan lamari ya kamani, hannu yasaka ya kwantar da kaina a k'irjinsa yana d'an buga bayana da d'ayan hannun, zanyi magana ya d'ora yatsunsa hannunsa uku na tsakkiya akan bakin alamar nayi shiru. banida za6in daya wuce yin shirun, nabisa yanda yakeso. Yanayin da zuciyarsa ke bugawa sai yabani tsoro, na saka hannuna na danne wajen sannan na d'ora kaina bisa hannun, ajiyar zuciya yayi yana cizar lips.. Tsawon mintuna 3 muna a haka, har knocking d'in k'ofa akayi amma baiko motsaba bai barni na motsaba, na yunk'ura zan tashi ya maidani. Munkai mintuna 7 sannan ya zameni ya kwantar ya mik'e zaune, batareda ya kalleni ba ya sauka daga gadon, bathroom ya Shiga, babu dad'ewa ya fito, nidai kallonsa kawai nake da mamaki, Dan fuskarnan amatuk'ar d'aure take tamkar baisan minene dariyaba a rayuwarsa, ya shinfid'a abin salla, domin rama sallolin da suka riskesa yana barci. 6oyayyar ajiyar zuciya na sauke, na tashi zaune idona akan yaran, duk sun koma barci, na tsurama Abdurraheem ido, saboda fitar numfashinsa ta banbanta dana y'an uwansa, tunani nai ko yanayin nasa barcin kenan shikuma, saboda wahalar da suka sha, d'aukar ledar kayan da mom ta kawo nayi, na fiddasu na saka, ban jira ya idarba na fice abina. Nayi mamakin da yanzu babu kowa, harsu Munubiya sun tafi, haushi ya kamani kamar zanyi kuka, aidai sa jira na fito mu gaisa ko? hawayen da suka zubomin a kumatu na share, namafi jin haushin Munubiya wlhy. Sallamar da akeyi na amsa da k'yar, sannan na bada izinin shigowa, cikin bayina ne guda biyu, zubewa k'asa sukayi suna gaisheni. Cikin girmamawa d'aya tace, “dama ance mu gani idan kin fitone”. Nace, “Hummm”. Fahinmatar iya amsar dazan iya basu kenan ya sakasu mik'ewa suka fita, zamewa nai na kwanta cikin kujerar ina cigaba da zirar da hawaye. Kusan mintuna 5 saiga Samha ta shigo, ta durk'usa gaban kujera tana sharemin hawayena, d'ago ido nayi na kalleta, namata murmushin k'arfin hali ina tashi zaune. Muryarta da alamun tasha kuka itama tace, “Aunty Uncle Sam na kiranki”. Kai na jinjina mata kawai, na tashi gaba d'aya na d'auki mayafi muka tafi tare. Koda mukaje k'ofar falon bata Shigaba, nikad'ai na Shiga ita kuma ta juya ta fice daga sashen gaba d'aya. A falo na iskeshi cikin doguwar kujera a kwance, ya kifa yaron d'aya a k'irjinsa Wanda nake k'yautata zaton Abdurraheem ne, wayace manne a kunnensa, amma a hankali yake magana koni danake tsaye cikin falon banaji, na kalli abincin da aka jere a tsakar falon ina zama a kujera. Bai dad'eba ya kammala wayar, idonsa dake jajir har yanzu ya d'ago yad'an kalleni, jijiyar kansa dukta tashi rud'u-rud'u. saida yad'an lumshe idanu kafin ya motsa la66ansa ahankali yace, “kici abinci inji inno”. Dukda maganar taban haushi haka na danne, wato inji inno ma ba injishi ba ko?. Sakkowa nayi k'asan lallausan carpet d'in, d'aya bayan d'aya na bubbud'e kulolin da kwanikan, a rai na ina tunanin ina zamu kai wanna abincin haka?. Tashi nayi zuwa ga show glass d'in dake falon, wadda aka jera mugs and glass cups, mug d'aya na d'akko, naje wajen wanke hannu dake a wajen dinning, Wanda babu tebirin cin abincin ba'a sakaba, bansan dalinsa nak'in sakawarba, wanko mug d'in nayi na had'o kayan tea a ciki dake a wajen show glass d'in suma, na zubo ruwan zafi daga dispenser na dawo, yana kwance yanda na barsa, yanzuma garda su lumshe idanu yanata shafa kan yaron zuwa bayansa. Na kallesa a d'arare Dan yaune karan farko dazan aikata hakan, komi yake buk'ata yakan yi da kansa, ko ruwa wannan inhar bana manta ba bai ta6a cewa na d'auka masaba, sometimes ma sai idan yasaka Samha ko Sauban su masa Abu saini na tashi nayi idan naga rashin dacewar hakan, amma dai dakansa yace Munaya yimin kaza, gaskiya bai ta6aba. muryata na rawa nace, “bismillah”. Shiru kamar bazai bud'e idonsa ba saikuma ya bud'e d'aya yad'an kalleni ya kauda kansa. cikin k'asaitar nan tasa yace, “miyasa?”. “miyasa kuma?”. ‘nakuma maimaita maganar ina k'ok'arin janye hannuna’. Carab ya rik'e hannun nawa, ni tsoroma ya bani, na kalli hannunsa da nawan ga mug cikeda ruwan zafi yanata turiri, kuma zafin yana ta6amin gwiwar yatsuna, idonsa a lumshe har yanzu, idona harya fara tara kwalla, nayi alk'awarin koda hannun zai toye gaba d'aya bazan tanka masaba, ai yasan abinda yake dai-dai da akasin haka. Saida mukayi 1minute a haka kafin ya maido face d'insa inda nake yana kallona, ya d'age gira d'aya yana fad'in “da zafi ne?”. Humm lallai Galadima akwai rainin wayo, na fad'a a zuciyata, janye idona nayi daga kansa na maida kan Abdurraheem dahar yanzu yake kwance a bisa cikinsa. Ya yamutse fuska yana sakin hannun, cikin basarwa yace, “inason jarumta”. Had'iye kukan dake k'ok'arin tahomin nayi, na ajiye Mug d'in na cigaba da zuba masa farfesu a k'aramin bowl batareda nayi koda tariba. Tashi yay zaune yana jije lips, yayinda hannunsa ke rik'e da yaron, d'ayan kuma ya dafe saitin zuciyarsa, a wahalce yake fisgo numfashi kafin ya fesoshi, tun kuma d'azu na lura da hakan, kalmar zafi daya fad'amin na shiga fassarawa, har na fahimci da manufa ya fad'a, hakanne ya Sani murmusawa batareda na d'agoba ina zuba masa farfesun nace, “tabbas duk zafi sunansa zafi, amma akan samu banbance-banbance wajen banbancesu, wani zafin a gangar jiki muke jinsa, wani ko tawani sashen jikin ake samunsa, wani zuciya, wani rayuwarma gaba d'aya Ce ke tsintar kan a zafi, saidai babu zafi mafi rad'ad'i daya kai na Mutuwa, idan da zamuyi nazari zamu fahimci rayuwa tana a tsare ne mataki-mataki, sannan iri d'ayace ga kowanne launin halitta na mutum ko aljan ko dabba, Dan mukan tainci kanmune akusan mizani d'aya, dukda ubangiji ya banbantamu ta halitta da ayyuka da tunani ko nace kaifin basira, ko'a jinsi launi biyune, akwai namiji akwai mace, dukkan rayuwa takan farane da mafari yalla6ai” na d'ago ina sake mik'a masa mug d'in tea d'in again, a mamakina a yanzu saiya kar6a, na lashi lips d'ina na k'asa ina gyara zama sosai da maida hankalina wajen juya kunun dana zuba a cup da tsokali, cikin nisawa nacigaba da fad'in, “mafarin rayuwa shine dasuwar bawa a cikin mahaifiya, mukanyi wannan rayuwarne a cikin halin su wanene mu? daga nan sai matakin haihuwa, shigowa duniya a bisa bigiren wane ahali muka kasance, dukkan ahalin daka Sani sunada matsalarsu, saidai tawasu tafi tawasu zafi, daga ranka ka iso filin gwagwarmaya wato duniya, shikenan littafinka dayazama rubutacce tun a cikin mahaifiya saiya fara aiki, mala'iku masu kula da fitar numfashi su dasa alk'alaminsu, masu kula da abinci suma haka, masu kula da ruwa ma haka, masu kula da magana ma haka, masu kula da kallo ma haka, masu kula da ji ma haka, masu kula da duk wani motsinka ma haka, tafiya, zama, kwanciya dadai sauransu, kowa ana haihuwarsa tsaftatatccene, iyaye suke fara juya akalar rayuwa, walau mai k'yau ko sa6aninta, (kaga kenan akwai hisabi tsakanin iyaye da y'ay'a ma kenan?) daga nan rayuwa zata cigaba da yad'o kamar d'an duma, tun ana maka, harka koma koya, harka fara iyawa da kanka, harma ka kware ka koyama wani, (wanne ka iya? ko ka koya? yarage ruwanka) duk Wanda kaga an masa a farko to tabbas za'a k'ara masa a k'arshe, kodai silar tsufa, ko ciwo, kokuma iftila'in rayuwa, kokuma na k'arshe shine hidimar gawarka, a dukkanin dunk'ulalliyar rayuwar da kowanne bawa yakanyi zakaga cike take da k'alubale masu zuwa da zafi kala-kala, yalla6ai kasan mike taushe wannan rad'ad'in zafin kuwa?”. nayi maganar ina d'ago ido na kallesa. A mamakina sainaga ya girgiza min kansa. na murmusa ina janye idona daga kansa na maida ga kofin tea d'in ina masa alamar yasha mana. Yamutse fuska yay irin kalar tausayinnan. Nima sainayi kwal-kwal da ido kamar zanyi kuka, na had'e hannayena waje d'aya alamar rok'o🙏🏼.. Lips d'insa yad'an ciza kafin yafara shan tea d'in. Nayi salute nashi ina masa jinjina👍🏻. Basarwa yayi, nima saina kad'a ido ina tunzura baki gaba, sannan nacigaba da fad'in, “Abinda ke taushe wannan rad'ad'in zafin shine *_HAK'URI_*. hak'uri muhimmun sinadarine dake jagorantar garkuwar jiki ta kowacce launin halittar jiki na d'an Adam, walau a fili take ko a 6oye take, saidai babban makarinsa da taskar adanashi shine *_ZUCIYA!_* a duk lokacinda k'arfin zuciya ya raunana to zaka samu madarar hak'uri ta salwanta, idan zafi yanata yawa babu wannan hak'urin bugu d'aya take duk wani ma'adani na cikinta saiya tarwatse, saikaga an rasa ayyukan jiki dana ruhi, shikenan wane yazama labari. daga lokacin da rad'ad'in fitar rai ya kusanci bawa dukkan mala'ikunan da suka kasance tare dakai a randa kazo duniya saisu fara janyewa daga gareka, wani bawan kafin ranar mutuwarsa zakaga ya daina cin abinci, hakan na nufin mala'ikan dake kula da abinci ka yagama aikinsa, domin ya zagaye duniya kaf duk yawan abincin dake cikin ta babu rabonka koda kwayan gero ne, ka gama cinyewa, wani kafin ranar Mutuwa ya daina shan ruwa, aikin mala'ikan dake kula da ruwa shanka yagama k'arewa kenan, duk yawan koramu da tafkuna na duniya bakada sauran rabo na ruwa, ka shanye naka, wani kafin Mutuwa ya daina magana, mala'ikan dake kula da furucinka yagama aikinsa, babu sauran wata kalma data rage harshenka ya furta, wani kafin Mutuwa ya daina ji, mala'ikan dake kula da jinsa ya gama aikinsa, babu wata kalma data rage kunnensa zaiji, wani kafin Mutuwa ya daina gani, mala'ikan dake kula da ganinsa ya gama aikinsa, kwayar idonsa bazata sake kallon wani abuba, wani kafin Mutuwa ya daina tafiya, mala'ikan dake kula da tafiyarsa ya gama aikinsa, haka-haka wad'annan mala'ikun zasuyita ja baya suma barinka, har yarage sai mai kula da fitar numfashi kawai, daga ranar da UBANGIJI yace yana buk'atar ganinka shikenan takuma k'are, sai rundinar mala'iku su had'u su takewa kwamandan mala'ikan d'aukar rai baya, idan kai mutumin kirkine fararen mala'ikune, idan na banzane mala'iku masu azaba zasu take masa baya, sauran al'amari kuma sai Wanda ya haliccemu yasan ya zata kasance😭. zakasha mamaki idanfa nace maka duk wannan zafin k'aramin zafine acikin kashi-kashin na abinda ya shafi haluttu, shi wannan zafin ana kiransa zafin na za6in kai, kokuma zafi na a haka tsarin yazo, ma'ana kaine ka had'ama kanka wannan zafin, kokuma wanine ya had'a makashi. Abu na biyu shine zafi na rad'ad'in Mutuwa, dolene kowa saiya d'an d'anashi, walau kafiri ko Musulmi, saidai akwai banbance-banbance na awanne tsari ka koma ga ALLAH, ba wannan zafinne kawai ke jiran d'an Adam ba, akwai zafin na *_BARZAHU_* shi ake kira kwanciyar kabari, mika tanada, mi zaka tarar shine abin tambayar, wannan kam ALLAH ne mafi sanin wad'anda zasu d'and'ana wannan zafin (ALLAH ka datar damu😭)”. Akan la66a Galadima ya amsa da amin, Munaya ta share hawayenta, ta cigaba da fad'in sai zafi mai gaba d'aya, shine na makoma, *_WUTA KO ALJANNA_*, yalla6ai wad'annan jimullar zafin ga d'an Adam tilas ne, na cikin rayuwa shine zafin da zaka iya controlling nashi ta hanyar hak'uri, to Ashe bai kamata ka tasirantar da wannan zafin ya cigaba da k'onaka ba, musamman idan zakayi dubi dawasu ni'imomin da ALLAH yamaka a cikin wannan zafin, ka kasance mai yawan hak'uri saikaga kanka cikin masu yawan riba, wlhy ta wannan hanyarne kawai zaka zama mai *_NASARA_* akan mak'iya ni..........”. Maganata ta katse saboda knocking d'in k'ofar da akayi, kallon juna mukayi ni da shi, yay wani luuu da idanunsa ya lumshesu, hakanne ya sakani bada izinin shigowa kawai batare da na jira amsa daga garesa ba. Sarkin k'ofane ya shigo, ya zube yana gaishe mu, nice kawai na amsa, boss kam hannu kawai ya iya d'aga masa, yay mana ya jiki again, nanma nice nakuma amsa shi, cikeda girmamawa yace, “ranki ya dad'e yalla6ai harun ne ke buk'atar iso”. Saida gabana ya fad'i, na had'iye wani yawu mai kauri ina kallon galadima dayay biris damu yanata shafa kan d'ansa, bud'e idonsa jajaye yayi akan Sarkin k'ofa, ya jinjina masa kai alamar ya shigo dashi. Kallonsa nayi tamkar zanyi magana saikuma nai shiru, a raina ina mamakin wannan munafukin dami yazo kuma?..... ban kai k'arshen zancen zucin ba Harun yay sallama, nid'ince dai na amsa cikin danne zuciya da fushina. Ya zauna fuskarsa d'auke da murmushi. Nima saina saki tawa ina fad'in, “barka da hantsi ranka ya dad'e”. “Barka dai gimbiyarmu, ya jikin ki dana yalla6ai?”. Na kalli Galadima dayay shiru kansan jingine da kujera ido a rufe, “da sauk'i”, na fad'a ina mik'ewa na koma saman kujera, dan bazan ta6a barin falonba sainaji uwarmi ya kawosa. Ya amsa da “masha ALLAH, ALLAH ya kiyaye gaba ya k'ara lafiya”. “humm” na fad'a ina amsawa da “Amin dai”. Hankalinsa ya maida ga Galadima, “Sameer ya jikin?”. Bud'e idonsa yayi shima, ya ajiye mug d'in hannunsa a teble d'in dake gefen damarsa, batare da yace uffanba ya sauke ajiyar zuciya yana taunar lips. Banga alamar damuwar rashin amsawar tasaba a fuskar Harun, dan yariga ya saba da halinsa. Saidai idonsa k'uri akan Abdurraheem dake cinyar Galadima d'in yana barci, mik'ewa yay yana fad'in, “my son zo mu gaisa ko?”. Ganin haka nima nayi azamar mik'ewa nakai ga Galadima kafin shi ya isa, na d'auke Abdurraheem d'in ina fad'in “ai barcima yake ranka ya dad'e”. Ba Harun ba hatta da Galadima saida yaymin kallon mamaki, nakoyi cid'in-cid'in da fuska yandama bazaice nabama Harun d'inba. Baki ya bud'e kamar zaice wani Abu saikuma yay shiru yana kauda kansa daga kallona, nima saina ta6e baki ina barin falon da harar Harun ta gefen ido. Gaban Harun ya fad'i, mi yarinyarnan take nufi?...... Kafin ya lalubo amsar ya tsinkayi maganar galadima yana cewa, “sorry Harun, kasan har yanzu a tsorace take, duk wani motsinsu akan idontane”. Murmushin basarwa harun yayi, yace, “ai dolene hakan ranka ya dad'e, abinne akwai tsoratarwa, wlhy jiya tashin hankalinnan ne yasaka azababben ciwon kai rufeni, shiyyasa ko ganina ba'ayiba, yanzu police d'in ina suka samosu?”. “humm” Galadima ya fad'a cikin tsananin taune lips da k'unar zuciya, ya bud'e baki a hankali zaiyi magana nida ke bayansu basu saniba nai saurin tareshi da fad'in “a hannun wasu munafukaine ranka ya dad'e, ai koni daza'a bani baiwar nan da aka kama da yaran wlhy saina tsoma kanta cikin drum d'in ruwa harsaita daina Numfashi zan barta, kafin sannan kuma nagamajin labarin Wanda ya sakata, amma shi my boss ai a station suka zauna har aka kawo yaran, badasu akaje farautarba”. Tsuramin ido Galadima yayi cikin tsagwaron mamaki, miyasa to zanzo na kasa na tsare dukkan wani motsin Harun d'in? ya kula satar yaran tana Neman ta6a tunaninta takasa banbance Wanda zata zarga, ai Harun yawuce ya 6oye masa wani sirri na sashen rayuwarsa, tun da babu abinda bai saniba na baya, saidai abinda ba'a rasaba kam, danne ransa yayi ya nuna hakane, yabari har Harun d'in ya tafi sannan yaji dalilinta. Ina kallon Sassanyar ajiyar zuciya da Harun ya sauke a 6oye, sannan yace, “ai police d'in sun cancanci Babar k'yauta, shiyyasama na shirya musu ita, sunyi aiki irinnan jaruman masu tsaro”. “hakane wlhy ranka ya dad'e ”. Na fad'a cikin murmushi. Dukfa yanda Harun yaso bugar cikin Galadima yaji yanda abun yake, na kafa na tsare, dayayi tambaya nike bashi amsa, saiya d'auka kodan Galadima bashida lafiyarne shiyyasa bai iya amsawa, tun da tunda ya shigo baice k'ala ba, kuma yasan yanayin ciwonsa, a baya ma shikan bashi taimako, baidai tsinci komai ba yay mana sallama ya fita, da k'udirin anjima ma zai dawo ne. A sace na raka bayansa da harara, sannan na kalli Galadima na basar, dukda kallon tuhuma dayake jifana dashi kuwa. Wani farfesun na sake zuba masa na mik'a masa. Batare da ya kar6aba cikin k'ank'ance idon bala'i yace, “mikikayi haka? kinsan waye Harun a wajena?”. Kaina na girgiza masa. Yaja tagwayen tsaki yana hararata, “halan satar yaranki yafara shafar tunaninki ne? kina tunanin akwai abinda Harun zai iya gazaji daga sirrina?”. Na d'an ta6e baki ina jawo teble d'in gabansa, na d'ora bowl d'in dana zuba farfesun, baki ya bud'e kamar zaiyi magana saikuma yay shiru. nima bance uffanba na ajiye masa sannan na koma k'asa Na zauna na zuba sabon kunu nahau sha. Kwafa yayi, yace, kinma maidani d'an iska ko?”. “Hummm” na fad'a kawai, naimasa kallo d'aya “yalla6ai wani karatun akan barsane a yanda yazo, sai idan lokacin fasaarashi yayi amasa fashin bak'i, nasan darajar alak'ata dakai batakai koda rabin tsakaninka da Harun ba, domin ni alak'ar wucin gadice ta had'amu, k'iris ma ya rage ta k'are, saidai inason nabama y'ay'ana kamar yanda ka fad'a kariya koda sau d'ayane a rayuwarsu kafin na barsu, dan haka maida wuk'arka a kube, lokacin zareta baiyiba, sometimes kalmar Mahangi da mai hange takanyi kamanceceniya, dan bakowa ke iya rarrabata wajen fasaara ba, amma kalmomine duka masu harshen damo, wani k'alubalen saida tunanin mai zurfi, wata k'oramar ruwan mutanen dake zagaye da ita sukanyi imani bazata balle harta cisu ba, saboda sun yarda sud'in masuntane da kullum suke rayuwa cikin wannan k'oramar, abin mamaki saikaga wataran an wayi gari da mutanen da muhalansu duk wannan ruwan ya had'iyesu, abinda basu ganeba bakowacce irin alak'a bace ake kulla amana da ita, wani farin idan yashiga cikin fari banbance k'arkonsa saidai ALLAH”. Tashi nayi nai shigewata bedroom d'insa. A fusace shima ya mik'e zai bini, kad'an yarage ya zubda farfesun dana ajiye masa, ALLAH dai ya kiyaye ya shallakesa ya wuce. Hucin mutum kawai naji a bayana, hakan yasani waigowa da sauri, hannu ya dunk'ule zai kaimin naushi, nai azamar fad'awa saman gadon ina zaro ido waje, a lallai Abu ya girmama, nikuma miye nawa da zai sauke fushinsa a kaina? nai maganar a zuciyata. Janye hannunsa yayi yana ciza lips d'in sa da k'arfi, idonsa dukya kuma rinewa, ya dunk'ule hannun ya daki d'ayan dashi, muryarsa har rawa take yace, “Miyasa zaki kuma hargitsan tunani ne? Minene laifin Harun shikuma? kuna nufin duk Wanda na yarda dashi shine mak'iyina? Kai impossible wlhy, Munaya wakikema aiki a kaina? ya rankwafo kaina, kaikace cinyeni d'anya zaiyi, saikace zaki yaga bandar nama, da k'arfi yace, “bazaki sanarmin ba saina k'arar da numfashinki ne waishin Ubanwa ke fad'a miki wad'annan maganganun da kike d'aureni dasu a ko yaushe?!!!”. Ya k'are maganar cikin tsananin tsawa da k'araji. Ba k'aramin firgita nayiba, badan karnayi k'arya ba danace har wutar bala'i Nagano a idonsa tana ci, wannan bawa akwai zuciyar tsiya, idan zai zama jami'in tsaro da k'asarmu ta amfanu da yawa......... Da k'arfi ya girgizani, saboda ganin saboda rainin wayo tunanima na tafi.......... A firgice nace “yi hak'uri zauna zan fad'a maka”. na fad'i hakanne dan kawai ina ganin itace mafitar dazan nema ya fasa had'iyeni. a mamakina kuwa saiya tashin ya zauna yana dafe k'irji hawaye nabin kumatunsa. Tsantsar tausayinsa ce ta kamani, na tashi na d'akko ruwa na dawo kusa dashi na zauna, addu'oi na shiga tofawa a ruwan, yana zaune dafe da kansa, da alama kuka ma yakeyi, dan ajiyar zuciyar da yakeyi ta yawaita. Saida na gama na dafa ka fad'arsa, tamkar bazai d'agoba saikuma ya kalleni, ruwan addu'ar na basa, babu musu ya kar6a ya shanye, duk da baima san mita bashiba, idanma poison ne dai gara ma yasha ya mutu ya huta. Mintunansa biyu zuwa uku dasha yafara sauke ajiyar zuciya mai k'arfin gaske, saiya zame kuma ya kwanta, kafin kacemi barci ya saceshi a haka. nima ajiyar zuciyar nayi ina girgiza kai da share hawayen dake silalomin, ina rok'on ALLAH ya kawoma wannan bawan nasa sauk'i da rangwame cikin gaggawa da warwarewar al'amura. Dagashi har yaran tausayi suke bani, nayi zurfi a tunani wayarsa tayi ring, kamar zan share saikuma Na tuna maybe Momma ce, tashi nayi zuwa inda wayar take, aikam dai itace, nayi picking jiki a sanyaye, dan tunanina kota gamajin komai, amma sainaji sa6anin haka, da y'ar raharta ma tace, “Muh'd duk hidimar sunance haka?”. “Uhm Momma bashi bane nice”. “a'a d'iyata kece?”. “eh Momma, kuna lafiya? ya jikin Abie?”. “Alhmdllh d'iyata, ya k'arfin jikinki kema? ina yaran?”. Gabana ya fad'i, Na had'iye wani yawu da k'yar, cikin in ina nace, “lafiyar kowa k'alau Momma, shima y... yana barcine”. Dagacan Momma ta murmusa tana gyara zama a harabar asibitin, dan batason Abie yaji wayar da zatayi, tace, “humm d'iyata kema 6oyemin zakiyi kenan? yanzu koda mutuwa yaran sukayi dashi kansa kowama saiya shiga fargabar gayamin?”. Na had'iye yawu dak'yar, “kiyi hak'uri Momma, ki gafarcemu”. “Bakumin laifin komaiba ni, hakan da Muh'd yay shine dai-dai, dan lokaci yayi dazai daina zama jiran sak'on mak'iya ko zuwansu, shine yakamata ya fita farautarsu domin kawo k'arshen komai, na yarda dake 100% Munaya, nakumayi imani insha ALLAH kece zaki sauyamin yaro daga k'uncin dayake ciki zuwa farin ciki, tamkar yanda Na fad'a miki tun farko karki ta6ama Muh'd sanya ko nuna tsoronsa, lokacin dazaki kwantar masa dakai kizama kowacce irin mace a agidan mijinta har yanzu baiyiba, kada ciwonsa yasakaki fargabar fad'a masa gaskiya, rayuwa da mutuwa duk Na ALLAH ne, ko ayanzu Muh'd yabar duniya bazanyi bak'in cikiba, domin ya nuna musu shi jarumine, kuma ya haifi wad'anda zasu iya zama magadansa su sauya komai koda ba'aso, nanda kwanaki biyu komai ya gama lafawa ki tabbatar kin masa maganar tafiya wanka gida, wannan shine target d'inmu Na k'arshe akan rayuwar zaman aure na dindin, kowacce irin birkicewa zai miki akan bazaki jeba, kema ki birkice masa, dan nasan abinda yafaru zaisashi dagewa akan yaran bazasuyi nesa dashiba, idan kuma har aka cigaba da tafiya a haka, kowane irin dana Sani zai iya biyo baya”. Momma ta share hawaye dake kwarara a idanunta, taci gaba da fad'in “ALLAH yayi miki albarka Munaya, dake da abinda kika haifa, yanda kikamin biyya wajen k'autata kar6ar Abu mai wahala (duk da bani na haifekiba) kema ALLAH yasa y'ay'anki sumiki biyyaya fiye da wannan, ALLAH yasaka hannu adukkan lamarinki keda mijinki da sauran y'an uwansa, nusar dashi abinda duk baki gamsu dashiba shine zai rage ma zuciyarsa baraza, dan tarawar yagani a lokaci d'aya shine mafi had'ari Munaya, zuciyarsa zata iya bugawa a lokacin, kiyi hak'uri nasan bak'yajin dad'in zama da Muh'd ko kad'an, domin ni kaina mahaifiyarsa wataran gaza gane kansa nakeyi, amma inaji a jikina akwai sauyi maiban mamaki dazai zo ya rusa komai, ki sameshi fiyema da yanda kikeso, ALLAH yayi muku albarka, idan ya tashi ki kirani naji ya jikin nasa”. Bata jira nayi magana ba ta yanke wayar, da alama kukane yaci k'arfinta. nima saina fashe da kukan ina kallon Galadima, insha ALLAH zan cikama baiwar ALLAHr nan burinta, koda ace mun rabu dashine, dan maganar gaskiya bazan iya rayuwa da mutum murd'ad'd'e mara yarda irin Galadima ba, labarinsa kawai kukeji, amma halinsa saika zuna dashi, Mara hak'uri zai iya gundurarsa ne cikin awanni biyu kawai, dan zaka dinga kallonsa a matsayin mai wulak'anci ko dizgi, girmankai da sauransu. Na sauke ajiyar zuciyarsa ina maida kallona ga Abdurrahman dake motsin tashi, nasan dukansu saisun tashi inhar d'aya ya tashi, saina lalla6a na kwanta kusa dashi na saka masa nono a baki. ******************** Har akayi la'asar Galadima bai farkaba, Nuren yazo shida Sauban, da Saleem har sau biyu suka iske yana barci, hakama Mom da inno da mama Fulani. Gashi su inno 4:30pm zasu wuce ma, laraba tazo tama yaran wanka, dan tuni sun farka, Nima nakumayi sannan naci abinci, kaina ciwo yakemin sosai, dan haka Sauban yafita ya samomin Magani nasha na kwanta, munyi sallama dasu Mom, zasu dawone kawai idan Galadima ya farka kafin su tafi. yaran kam duk d'insu suna can an kaima papi su tun d'azun. Nidai barci yay awon gaba dani, daga nankuma bansan wainar da aka cigaba da toyawa ba a gidan. ******************* Bayan la'asar kad'an Galadima ya farka, ganin shi kad'aine a d'akin ya tashi zaune bakinsa d'auke da addu'ar tashi barci, jin k'irjinsa yayi sakayau yasaki babu nauyin kamar d'azun, saidai abinda ba'a rasaba, yatashi zuwa bathroom yay wanka da alwala. Sallan zuhur da la'asar ya rama, tareda addu'ar neman sauk'i akan wannan lamari da samun k'arfin zuciya, dolene saiyayi yak'i da dukkan abinda zai zama makamin barazana a agaresa inhar da gaske aikin zaiyi, falo ya fito bayan ya kimtsa, zamansa da mintuna baifi 2 ba saigasu inno. Basu jira isoba suka shigo, a zatonsu yana bedroom yana barci, sunsan Munaya kuma tana d'akinta tana barci tunda daga can suke. ganinsa a zaune ya saka fuskar kowannensu fad'ad'a da murmushi. Shidai kallonsu kawai yake d'ai-d'ai. Inno ta mangari kansa tana fad'in “ja'iri baka sanmu bane halan?”. Hannunta ya rik'e yana kallonta, cikin maganarnan tasa ta k'asaita yace, “Inno wai ina zakuje ne?”. “inda muka fito mana”. Inno tafad'a tana zama kujerar kusa dashi. “saikace wad'anda ake kora?”. “A'a wazai koremu nida gidanmu, komawar dai ne yafi cancanta, dan takawa ma yace a gaisheka basai ya shigoba, zakuyi waya, idan ka murmure kaje yana nemanka”. “To shikenan ALLAH ya tsare hanya, mun gode sosai da sosai”. “Amin” inno tafad'a tana shafa kansa ta ciga da kwararo masa addu'oi shida matarsa da yaransu, falon kowa tana amsawa da amin, itama mom tayi nata. Yace, “mom hada ke wai?”. “eh mana Sameer, zaman mi zanyi to? tunda ALLAH ya iyakance komai cikin sauk'i, nanda y'an kwanaki kuma basai na zagayo naga masu jego ba da jikin naka, a dai dunga kulawa sosai, gasu laraba nan da bayi 2 anbar muku, dukdai wata kulawa insha ALLAH zasu taimaka wajen badata akan yaran, dan yakamata dukkan bayi da kuyangin sashen nan naka ka sallamesu kawai”. Kansa ya jinjina mata alamar amsawa. A gurguje sukad'an kuma tattaunawa da kwantar masa da hankali suka fito, dukda yaso musu rakkiya suka dakatar dashi. Abincin da mom ta zuba masa takumace yamata alk'awarin zaici ya dage yaci sosai, sannan Sauban daya dawo rakkiyarsu d'auke da y'an uku shida bayinnan biyu yabashi magani yasha, kar6ar Amaturrahman yayi, Sauban kuma na zaune dasu Abdurraheem yana musu wasa wai dole sai sunyi dariya, (nace, “aiki jaa kenan, inba dariyar k'udaba ta jarirai idan suna barci keyi aiko ka dad'e baka ganiba Uncle triplets😂). Galadima ma madai yatsansa d'aya ya saka cikin hannun Amaturrahman yana wasa dashi, dukda idonsa a lumshe yake ya jingina kansa da kujera, maganganun Munaya na d'azun kawai yake nazari dalla-dalla. Ana cikin haka Samha tayi Knocking, Sauban yace ta shigo, saida ta gaida Galadima damasa ya jiki. Ya amsa mata batareda ya kalleta ba, tareda tambayarta Khaleel fa?. Tace, “yana 6angaren Ummu hasheem”. Baice komaiba, itama ta k'araso ta d'auki Ammaurrahman data rik'e yatsansa gam tak'i saki.. d'agowa Galadima yay yana kallon yarinyar, Samha dai dariya takeyi, har Sauban shima ya farga da abinda ke faruwa ya shiga tayata. Galadima ya zare yatsansa yana murmuahin gefen baki da lakatar hancin Amaturrahman. Har Magriba suna nan sun shashance akan yaran, yayinda Galadima ke zaune yanata cud'awa da tantancewa, lokaci-lokaci yakan kallesu dagasu har yaran. Tunda ya tambayesu Munaya sukace tasha Magani tana barci bai sake tambaya ba. ******** Ban tashiba saida suka fara kuka, a time d'in har magrib tama wuce, nagama shayar dasu na lek'a Galadima, na iske doctor jalal tareda Dr Yaseen da Akash Wanda yake shirin komawa gobe, sai Muftahu da Nuren. Muka gaisa dasu suka kuma tambayata jikinsa? na Amsa musu da Alhmdllh. fitowa nayi na barsu, da aka kawo mana abinci ma can nace akai musu, Sauban yazo ya kwashi yaran bisa Umarnin Galadima, doctors zasu kuma duba lafiyarsu. ★★★★★★ Tunda Harun ya fita saiya kira wata Number lokacin daya k'arasa d'akinsa, dukkan abinda ya faru ya labarta mata, daga can tace k'aryane bahaka akaiba, ita an sanar mata lallai da Galadima aka kar6o yaran, babu wasu police, amma itafa kamar tafara saka alamar tambaya akan wannan ficikar matar tasa. Harun yace, “haba dai, wannan y'ar yarinyar mizata iya, akwai dai abinda bamu saniba, yanzu dai kibari zamuyi maganar daga baya, zand'an bincika yarannan danni na lurama kamar ba wad'anda muka saka bane sukayi aikinnan?”. “sunefa gaskiya, abinda dai na lura dashi sun had'a aikin da wasune, shiyyasa suke 6oye mana Kansu, tunda kaga mudai baiwarnan bamu muka sakata ba, amma shi namijin yana cikinsu, nasan sunyi luff ne sai k'ura ta natsa su fito”. “ok shikenan to, zandai sake bincikawa, dan Sameer yanada wayo, shiyyasa naso bugar cikinsa akan batun, amma wannan shegen k'asaitar tasa ta rainin hankali ya hanashi tankamin, sai matarce ke bani amsa”.. “karka damu zamu sauke masa shine ai”...............✍🏻 🤣abin dariya, ku a naku zaton yaranku sun 6oye Kansu be?, to suna hannun Galadima, lafiya kawai muke jira ya samu ya yagalgalasu kuma ya cafkoku munafukai🙄😏. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu._*😭🙏🏼 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣9⃣ ..............Harmun kwanta zuciyata ta kasa samun nutsuwa, inason naje naga halin da yake ciki, Dan koda su Nuren suka wuce ban komaba, sakkowa nai daga kan gadon, laraba dake a tsakar d'akin kan katifa tace, “ranki ya dad'e lafiya kuwa?”. Banason ta kalli abun da wata manufa, dan haka nad'an murmusa, “uhmm iya inason duba Abbansu ne, ban saniba koyasha maganinsa kafin ya kwanta”. “eh lallai hakan yanada k'yau, badan ma jego ba ai bai kamata ya kwana shi d'ayaba”. “aiba shi kad'ai baneba iya, Sauban ne zai tare dashi ”. A to hakan yayi. Bance komaiba Na kar6i gyale wajen Samha Na saka na fita. Masarautar tayi tsit, da alama kowa yasamu nutsuwa a sashensa, ban tsaya knocking ba na shige kawai, a falo na iske Sauban zaune yana kallon ball, cikin tsokanar da ya iya yace, aunty gimbiya kin kasa barcine?”. Nayi murmushi, “yaa Sauban matarka taga ta kanta wlhy”. Dariya yayi kawai, nikuma na wuce abina. Saida nayi sallama kusan uku banji an amsaba, saina shige kawai. Zaune na iskeshi a bakin gado ya jingina da fuskar gado, hannunsa d'auke da Qur'an yana karatu a hankali, idonsa cikin medical glasses, gakuma system a gefe itama a kunne. naji dad'in yanda na sameshi, Addu'a da karatun Qur'an babban jigone dake wanke zuciya da damuwar d'an Adam (duk lokacin da ranki ya 6aci d'auki Qur'an ki karanta koki saurara, wlhy zakuji sassauci mai yawa). Har zan juya na fita sai naji yay gyaran murya, juyowa nayi na kallesa, har yanzu dai karatunsa ya keyi. na dawo na zauna a bakin gadon ta d'ayan gefen, shikuma ya cigaba da karatunsa, kusan mintuna 6 kafin ya rufe Qur'an d'in ya ajiye, ya cire medical glasses d'insa shima ya ajiye yana kallona, ko kad'an fuskarnan babu walwala, nuni yamin da inzo. Ban musaba na tashi nadawo 6angaren inda yake, zama nai d'an nesa dashi kad'an. Ya lashe le6ensa da cizarsa kad'an yana hard'e hannayensa a k'irji. Muryata can k'asan mak'oshi nace, “yaya jikin?”. Kansa kawai ya jinjina min cikin lumshe ido, sannan ya motsa baki kamar zaiyi magana saikuma yay shiru, saida yaja wasu seconds sannan yace, “Munaya!?”. “Na'am”. Na amsa ina kallonsa da janye idon lokaci d'aya saboda ya tsareni da nasa. Huci yad'an furzar, ya cire hannayensa daga k'irji yana gyara zama, “Nayi nazaci sosai akan maganganun ki na d'azun, nakuma fassarasu aji-aji, na fahimcesu a yanda tawa fahimtar take, so a wannan karon rok'o nake miki na k'arshe akan ki fad'amin abinda kika sani, ni d'an Adam ne, ban isa cewa komai na sanshi a rayuwaba ko na iyashi, sai abinda Ubangiji yaso in sani kawai, Munaya ada ba haka rayuwata takeba, mutumne ni mai yawan raha dason nishad'i, amma daga lokacinda nafara sanin kaina da matsalar mahaifina sai komaina ya canja, nazama mutum mai yawan rashinson magana, nafison kullum na kasance ni kad'ai a kuma ke6antaccen waje” yay murmushin takaici sannan ya cigaba da fad'in “Bawai hakan Na birgeni baneba ko a San raina, saboda Ina shiga k'uncine, amma banida za6in daya wuce hakan. nasha wahalhalu Na rayuwa kala-kala kafin na tsaya da k'afafuna, zuciyata ta bushe namance daga wane tsatso na fito, domin idan kinganni a lokacin da nake karatu da koyan sana'oi bazaki ta6a kawo ni jinin sarauta baneba, ko d'an wani, nayi gwagwarmaya sosai irin wadda d'a Mara gata yakeyi, badan mahaifiyata bata sona bane ta tsaya tsayin daka wajen ganin na horu kona nemi na kaina, hikimarta itace nazama jarumi mai yawan juriya, nakuma kwato mana y'ancinmu a lokacinda ya dace, duk wannan fad'i tashin da kikaga inayi wlhy badan nayi mulki baneba kamar yanda su suke tunani, Burina kawai nasan miyasa aka durk'usarmin da mahaifi? Tabbas ni jinin sarautane gaba da baya, kuma yana yawo a cikin jinina, amma rashin kwanciyar hankalin dake cikin sarauta baya birgeni, kallon kitse kawai akema rogo, ayau inason Kituna kema kin haifi yaranda sun rigada sun shigo cikin wannan harmutsi, tunda tazama jininsu, ki fad'amin kodan mu gyaramusu gobensu su rayu cikin salama koda bama numfashine, nasan hakanan bazakima Harun abinda kikai masa d'azunba saboda son zuciya kawai, please miyasa kika hanashi d'aukar Abdurraheem ne? Miyasa kikak'i barina na fad'a masa gaskiyar abinda ya faru?”. Shiru nayi nakasa cewa komai, sai faman had'iye abinda ya tsayamin a mak'oshi nakeyi, Dan bansan yanda zai kalli abunba koya fahimceshi, babu Abu mafi saka rud'u irin cin amanar makusanci, gashi dai a Ransa shifa ba k'aunarka yakeba, amma kulum yafi kowa kusanci da kai, da Nuna girmama alak'ar tsakaninku. (ALLAH ka Shiga tsakaninmu da duk wani Wanda yake tare damu a matsayin fuka biyu, Dan yanzu abinda yafi komai yawaita kenan a rayuwar d'an adam☹😭). Cikin katsemun tunani Yace, “please my friend say Something mana”. Kaina na jinjina masa, cikin nutsuwa nafara masa bayani, Dan yau nayi alk'awarin sanar masa komai, koda zai samu wani haske akan lamarin, shima yasamu nutsuwa a rayuwarsa. “Tabbas kamar yanda kake zargi aiki nakema wani, saidai fahimtar wanene d'in shine mai wahala, na fad'a maka tun farko a dalilin bak'on Abbanmu naji wani yankin matsalasa da bai ta6a sanarma waniba a ahalinsa, a lokacin da wancan abin yafaru Abba yak'i fad'ama kowa dalilin fishinsa a kanmu, dakuma abinda muka masa, hakanne yasaka innarmu zuwa tasamu baba mai kanwa abokin kakanmu na k'ut da k'ut ta sanar masa fushin da mahaifinmu keyi damu, ankuma bashi hak'uri yak'i sauraren kowa, gashi ba dad'in zama takejiba cikin matan gidanmu, wannan Abu daya faru sai sukejin dad'i damata arashi da habaici, harma damu kanmu. baba mai kanwa yace taje zai masa magana, bayannan bamusan misuka tattaunaba. Sai da bayan komai ya lafa harma mun fara karatu sai sanata halluru ya buk'aci abbanmu yabama y'ay'ansa biyu auren yara cikin yaransa, sunzo gidanmu har suka nuna mune za6insu, a lokacin tabbas naji a raina Sa'eed yamin sosai a rai.....” Galadima ya tsuk'e fuska yana taune lips dajan k'aramin tsaki. 'Dagowa nayi nad'an kallesa, amma saiya basar tamkar bashine yayiba, nima sharewa nayi na cigaba, “bamusan miya faruba sukace Zarah da siyama sukeso, wannan Abu ya 6atama Abbanmu rai, dan aganinsa anyi wani abune domin k'untatama mahaifiyarmu, hakkane yasashi zuwa ya sanarma Baba mai kanwa, dama duk dai wani Abu dazai taso gidanmu shine ake sanarmawa, yayi sasanci koya tsawatar, koda kuwa innro ce. bayan Abbanmu yaje da kwana d'aya, sai innarmu ta aikemu wajensa muka kaimasa goro da y'ar sayayyar da takan masa lokaci-lokaci, saboda yamusu hallaci a rayuwa a yanda take bamu labari, shiyyasa a kullum take d'aukarsa uba”. Mun iske baba mai kanwa a d'akinsa na zaure kamar ko yaushe, muka gaidashi cikin girmamawa da tsokanarsa a matsayinsa na kaka, shima ya tsokanemu tareda sakamana albarka kamar yanda ya saba, saiya murmusa tareda gyaran murya, hakanne yasaka muka nutsu dan fahimtar magana mai muhimmanci zaiyi, ya nisa cikin dattako na tsufa ya fara fad'in___”. _“yarana kuyi hak'uri da damuwar da kuka tsinci kanku a ciki, wadda tunkafin Ku mahaifiyarku a ciki take, amma nasan watan watarana kuda ita duksai kunci ribar wannan hak'urin, karkuyi bak'inciki akan hanaku wannan auren da akayi na y'ay'an halluru, dama can sud'in ba mazajenku baneba, hasalima aurensu ba alkairi baneba”._. “A razane duk muka kallesa baki bud'e”. Yayi murmushinsu na manya, _“abin ya baku mamaki ko? Humm ba abin mamaki baneba, yau zan fad'a muku wani sirrin dabaku saniba, domin ina hango wani tarin alkairi tattare da rayuwarku, inakuma ji ajikina kune wad'anda zaku fidda mahaifinku daga wata sark'ak'iya daya Shiga a dalilin taimako tun kafin a haifeku. Alhaji halluru da wata manufa ya nema ma y'ay'ansa auren d'iyan mahaifinku, amma Shifa na fuskanci bai fahimci hakanba, sabo da ya aminta da amintar dake tsakaninsu ta tsawon shekaru. Alhaji halluru yanason shiga jikin mahaifinku ne sosai danya kar6ama iyayen gidansa wani sirri dake hannun Auwalu, ina k'yautata zaton shine kukaji wani Abu a ciki, shi kansa Auwalu baisan minene a ciki ba, domin kuwa bashi akai amana ya Isar dashi ga Wanda yadace, kuma baita6a yunk'urin ya duba ba ya barsa a yanda aka bashi. Kuyi hak'uri akwai wasu k'alubale dake tunkaro rayuwarku, kuma yanada tsananin sark'ak'iya, saidai insha ALLAH zan baku dikkan gudunmawa inhar ALLAH yabani tsawon ran kaiwa wannan lokacin, Ku dage da yawan sadaka kudai da mik'a lamuranku ga ALLAH mai kowa da da sirrin komai, ALLAH kuma ya cigaba da tsareku.”_ “duk cikin tsantsar damuwa muka amsa masa da amin, haka muka baro gidan jikinmu duk a sanyaye, dan har innarmu tata bincikarmu a lokacin, sai muka fake da ciwon mara. sati biyu da faruwar wannan lamari sai Munubiya tafara min k'orafin yawaita mafarkin wani bawan ALLAH, kullum takan gansa ne a cikin dokar daji zagaye da wasu irin halittu masu ban tsoro suna kaimasa hari zasu halakashi, yakanyi k'ok'arin kare kansa amma saiya gaza, idan yanemi taimakonta kuma bata zuwa, saboda tsoro suke bata. Duk sanda tafad'amin wannan mafarki sainace bata addu'a ne, shaid'anune kawai. haka taita jera wannan mafarki kullum dare, kuma da gari ya waye bazata fasa fad'aminba, tundai abin na damunmu har muka watsar muka cigaba da harkokinmu. Ranar kuma sai nima nayi mafarkin makamancin na Munubiya, saidai nikuma na shige ina taya wannan mutumin kare kansa ga wad'annan halittun kamar yanda ya buk'ata, na jigata sosai dan harnatashi jikina duk yayi week, nima ban 6oyema Munubiya komaiba na sanar mata, abin yabata mamaki, kuma tundaga sannan nima na cigaba da mafarkin, kullum kuma ina taimakon wannan mutumin dako fuskarsa ban ta6a ganiba, itako Munubiya takan cemin saidai ta tsaya kallonsa daga nesa yana bata tausayi, kuma yana shan nuna mata tazo ta taimakesa, amma saitak'i ta nok'e kafad'a. nikam a nawa mafarkin duk lokacin da ya nuna na taimakesa nakanje nashiga muyita fama da wad'annan halittu, ita Munubiya tana ganin fuskarsa, amma da zaran ta tashi, saita manta, niko ban ta6a ganin fuskarsa ba ko sau d'aya. Muna cikin halin wannan mafarki ne aka shiga bikin salla, tabbas randa muka had'u dakai a asibiti sainaita jin haushinka akan dalilin da ni kaina nasan bai isa daliliba, (dan kawai ina maka kallon mai girman kai bai kamata naji haushinka ba, tunda bawai hud'ace ta had'amuba, banikuma da tabbacin akanka abbanmu ke a had'ari), saidai had'uwarmu ta filin idi tasha banban data asibiti, dan a filin idi tsoro-tsoro mai gauraye da mamakinka ne suka zaunemin a zuciya, bayan kabani wayarka kabar wajen inata mamaki da juyata da tambayar kaina kaid'in wanene? Sai wata murya ta bani amsa da cewar *Galadima!* saidai koda na waigo banga kowaba sai alamar gittawar mutum mai jajayen kaya, na dad'e soaai wannan al'amiri bai bar rainaba, a haka muka shiga shagalin bikin y'an gidanmu, harda kuma su siyama, anan ne muka had'u da Fu'ad, harga ALLAH bansan wanene Fu'ad ba, bankuma San daga wace tawagar ango ya fitoba, amma amamakin kaina lokaci d'aya na aminta dashi, dukda kasancewata mutum mai masifar tsarta, cikin kwana d'aya kacal na saki jiki dashi, dukda ban amsa masa Cewar na kar6i soyayyarsa ba, daga ni harsu Ayusher bansan miya shiga kanmu ba muka yarda ya kaimu birnin gayu plaza ba, dukda kowannenmu ransa akwai fargaba, musamman ni danakeji kamar akwai wani gagarumin Abu dake tunkaro rayuwata. hardai muka shiga muka fito abinda ya faru ya faru a tsorace nake. fitowar wannan jarida a washegari yasaka dukkan wani ahalinmu a rud'ani, Wanda bansan yazan musalta makashi ka fahimtaba, lokaci d'aya da akazo bincikar wacece a cikinmu na amsa, dan jinai bazan iya bari Munubiya ta amsa laifinba, saboda tanada hak'uri, amma tanada tsauri Wanda nikad'ai da mahaifiyarmu muka San wannan tsaurin nata, dan sometimes takanyi mugunta amma tayi tamkar ba ita baceba, kai tsayema sai'a zargeni ita ba'ayi tunanin zata iyaba....” Galadima ya katseta da fad'in, “kina nufin bakece kika kusa fad'iwaba a plaza?”. Nad'an murmusa ina gyaran mayafina dake zamowa saboda kayan sunada santsi, “tabbas bani baceba yalla6ai, Munubiya ce, tausayi. Y'ar uwata yasani kar6ar laifin. Bayan wannan Abu ya faru nanma kowa yata fushi damu musamman Abbanmu, haryace saina nemo miji cikin 2weeks kacal, wannan ya d'agamin hankali, dan nikam kaf samarina babu Wanda yamin, amma sainaga kamar zan iya auren Fu'ad, wannan dalilin yasani kiransa bisa shawarar su feena, amma saiya toshe sukkan hanyar dazamu iya yin magana. bansan yazan misalta maka halin dana tsinci kaina a tsakaninba, naji natsani Fu'ad matuk'a, a wannan time d'inma na cigaba da wancan mafarkin, amma yazomin dawani sabon salo, sannan ita kuma Munubiya ta daina, mafarkin ya canjane zuwa salon da mutumin kanyi yunk'urin ta6ani, amma nakan hanashi damar hakan ta hanyar ja baya da masa gargad'i, shikuma saiya ringa rok'ona da cemin karna masa haka, ni fitilarsa ce. Har sannan kuma still bana ganin fuskarsa, abubuwa da yawa sun had'u sun dagulemin, dukna fige na fice hayyacina. A lokacin da baba mai kanwa yaje dubani asibiti bayan maganar aurenmu da haidar ta rushe saiyake magana cikin murmushi, k'asa-k'asa kuma ta yanda wani bazai jimu ba”. _“Ki kwantar da hankalinki Hussaina, har yanzu dai mijinki bai kai ga zuwaba, kuma bayan wannan ko 10 zasu k'ara zuwa saisun barki, dan akwai k'alubale a gabanki kafin kisamu nutsatstsiyar rayuwa._” “Da mamaki na kallesa, amma saiyak'i bani damar neman k'arin bayanin komai a wajemsa. Bayan na warke nadawo gida kuka saka aka saceni kaida Muftahu, na koma gida mangariba ta rufa a ranar, ashe wai baba mai kanwa yaga sanda na shiga gida a firgice, sai'a washe gari ya aiko a kirani, innarmu da Munubiya sunyi mamakin kiran, dan cayay Hussaina taje, (shi dama baya kiranmu Munubiya da Munaya, sai Hassana da Hussaina). Haka na saka hijjab naje, a yau baiyi wasan daya sabayi da niba, kai tsaye yafara maganarsa”. _“Hussaina jiya daga ina kika dawo a firgice?”._ “A tsorace na kallesa, dan lallai tsohonnan yafara bani tsoro, dama tun muna yara mukanji ana cewa tsoronsa akeji, saidai bamusan manufar tsoronba, murmushi yayi yana gyara zama da cigaba da gyaran wasu takarsu Dana tarar yanayi, yace___”. _“karkiji tsoro, nimai taimakonki ne gwargwadon abinda ALLAH yabani ikon sani, dan haka ki fad'amin gaskiya_”. “dak'yar na iya had'iye yawu, sannan na fad'a masa abinda yafaru tsakanina daku. Murmuahi yay mai matuk'ar sauti, wanda ya bayyana fararen hak'oransa da basu wuce goma sha ba da suka rage, wad'anda a kullum zaka sameshi da ashuwaki yana d'abbak'a sunna, yace___”. _“Hussaina ni bazance ki amince ko karki aminceba, saidai nabaki dama kije ki duk'ufa rok'on ALLAH, a cikin kwana ki biyu rak ALLAH zai nuna miki mafita da abinda zai zama alkairi a gareki, sannan karki sanarma Hasaanar ki, danna kula bazata amince ba tacikin sauk'i, tashi kije”._ “A wannan ranarma haka baba mai kanwa ya sakani cikin rud'ani, nazo dukna hana kaina nutsuwa da kwanciyar hankali, saidai nabi shawararsa ta mik'a kukana ga Ubangijin al'arshi, dan shine gatana kuma fitilata, a kwana na biyu kuwa saiga dalilin dayasani amincewa da buk'atarka ya faru, na amince maka badan hankali na ya kwantaba. tunda kuma lokacin baba mai kanwa bai kuma min maganar data shafi auren ba, harma na d'auka duk mafarki nayi, har maganar da mukayi d'in dakai. Saida ana gobe d'aurin aurenmu da safe na fita yin wani Abu na gamu da baba mai kanwa, shine yace na biyoshi gida. Mun Isa gida a d'akin zaurensa, yabani wasu abubuwa dabansan mineneba na sha, sannan yabani turare kashi biyu, yace ni 1 Munubiya 1, yace____” _“Hussaina kimin wata alfarma mana?”._ “A sanyaye nace kabani Umarni akwai baba. Yay murmushi da fad'in___”. _“ALLAH ya yimiki Albarka Hussaina, ina tausayinki ta wani fannin, ta wani fannin kuma murna nake tayaki, duk abinda nake hasashe a kanki nasan zaki iya, dan kinfi y'ar uwarki wayo, ni dake zamu had'a kaine wajen fidda mahaifinku a sark'ak'iya, su a gangancinsu sun tozarta kune domin tunzura mahaifinku da karyar masa da zuciya, amma basusan Ubangiji mai hikima baneba, yafisu sanin akan abinda su bai basu damar saniba, kiyi hak'uri inata miki magana a cirkud'e, zaki fahimci komai anan gaba kema, alfarmar da zakimin shine dukkan abinda kikaci karo dashi a rayuwar aurenki ki sanar min shi, insha ALLAH Zan miki fashin bak'i gwargwadon abinda na fahimtar nikuma, maganar zaman aurenku da yanda kuka ginashi kuma ya rage naku bayan warwarewar komai, wannan ba hurumina baneba, tashi kije, daga nan dai zamu dinga tayaku da du'ai”._ “Dukda banida tabbacin mijin dazan aura wannan magana tashi tamin nauyi da wahalar fasaara, da y'an gidanku suka kai lefena kuma saina kuma tsintar kaina a rud'ani da firgici, ban kuma fita daga wannan firgicinba har aka kawoni wannan masarautar. Saka pills da Muftahu yayi mana shine k'alubale na farko dana fara cin karo dashi Wanda nake k'yautata zaton baba mai kanwa ya hangomin, hakanne kuma ya sakani tada hankali nace nafasa auren, dan a zatona kun had'a bakine da Muftahu, amma sai maganar tafiya India ta datse dukkan hanzarina, ko kad'an banyi yunk'urin sanarma baba mai kanwa wannan batunba, dan aganina baya cikin abinda shima zaiso Sani. Idan baka mantaba a lokacin da ka kaini sallama gida da kuma gidansu Munubiya ka barni a can?”. Kansa ya jinjina mata idonsa a lumahe ya jingina da gado, kai kace ba saurarenna yakeba barci yakeyi. Ajiyar zuciya na sauke, na cigaba da fad'in “Aunty Salamah tazo gidan ta sameni ai, saboda Munubiya ta sanar mata zaka tafi dani, wannan itace damar farko dana samu na rok'onta yimin bincike akan Muftahu da Saleem yaronka na plaza, (abinda yasa Saleem yashiga Layin zargina saboda randa abinnan ya faru bayan fitowarmu shikuma naga ya fito daga tsakanin wasu motoci a firgice, dayake a time d'in bamusan mizai faruba ban kawo komai a rainaba sai washe gari, danayi bincike a kansa saina gane yaronkane na shago kuma amintacce) daga ita har Munubiya a lokacin basusan dalilina nason amin bincikenba, saidaga baya Munubiya ta fiskanci komai, dayake tanada kaifin basira, amma batasan tsakanina da baba mai kanwa ba. mun tafi India nabar Aunty salamah da wannan aikin”. Knocking k'ofa da akayine ya saka Munaya yin shiru bata cigaba ba, na kalli Galadima da har yanzu idonsa a lumshe, batareda ya bud'eba yabada izinin shigowa, yasan dai bazai wuce Sauban ba. Samha ce ta shigo, ta risina tana gaidashi, sannan tace, “Aunty Amaturrahman ta tashi itada Abduraheem”. Yunk'urawa nayi zan mik'e galadima ya katseni ta hanyar fad'in “jeki kawosu”. Na kallesa da mamaki, yayinda Samha ta fice abinta, “amma yalla6ai darefa yayi, mubari mu k'arasa zuwa gobe mana?”. “uhm-uhm”. Kawai ya fad'a. Shiru nayi nakasa cewa uffan, har Samha da Sauban suka shigo d'auke da yaran duka uku, kar6ar Abdurraheem nayi, dan yaron tausayi yake bani saboda rashin kuzarinsa (karku manta har Yanzu Munaya batasan yaron yanada irin ciwon mahaifinsa ba), su kuma Sauran ya kar6esu. Sauban da Samha suka fice sudai suna tunanin wannan zaman nasu, komi suke tattaunawa oho. Bayan fitarsu a cikin gyale na fara shayar da yaron, Galadima dai baice dani uffanba, sai kallon yaransa kawai yakeyi, na cigaba da fad'in “Abu na biyu dana fara cin karo dashi shine ganin Abie a halin daya tsinci kansa, wannan lamari ya d'aga hankali na, amma a lokacin banida wayar kiran baba mai kanwa na sanar masa, ina tsoron na saka a wayarka kuma ka gano wataran, sai kuma tarihin masarautar nan da Momma ta bani.......” Cikeda mamaki Galadima ya kalleta, dak'yar ya bud'e baki cikin yamutse fuska yace, “Momma!?”. Nace, “eh lallai Momma da kanta, dukkan rayuwar dakasha ta gwagwarmaya ta sanar min, tundaga yarinta zuwa girmanka, ta sanarmin hakanne danna lura da abinda ban saniba a masarautar, kar wani yayi amfani dani wajen cutar dakai. Bayan nan babu dad'ewa kabani waya, daga nan nasamu damar sanarma baba mai kanwa sirrinan guda biyu, ciwon Abie da tarinku. shine yabani dukkan addu'oin da maganin daza'a nema arink'ama Abie, kuma Alhmdllh munakan ganin haske. daga nan kuma na cigaba da samun haske game da dukkan Motsin Muftahu, amma kuma babu wani abinda bai daceba ko cin amana tattare dashi, damukaga mun shiga kokwanto saimuka saka Sarkin Mota da Saleem suka sace manashi a randa kaje d'akkomu a airport ni da Sauban lokacin da Abba yay accident ”. “ya salam! Kina nufin kece?”. Murmushi na masa, nace, “kwarai nice, hakan shine kawai mafita agareka damu kanmu, dan satar nashi ya zame mana haske, aunty salamah taje masa a amatsayin d'aya daga cikin matan Abie, ta hakanne kuma muka ji sunan Harun a bakinsa. daga nan muka sakama Harun ayar tambaya, su Ameer suka cigaba da bibiyar Harun d'in, kayi hak'uri ka gafarceni da abinda zan fad'a yalla6ai”. ‘nai maganar ina kwantar da Abdurraheem na d'auki Amaturrahman dake cinyarsa, itama na fara shayar da ita. “ki fad'i komi ke bakinki, na shirya kar6arsa da makamin HAK'URI”. Murmushi nayi cikin nisawa, “yalla6ai akwai sirrin dabaka saniba Wanda ya banbanta Muftahu da Harun, Muftahu shine masoyinka na gaskiya, Harun kuwa akwai manufar ra6arka tattare dashi, yasan kuma komai game da satar yarannan, akwai dalililai masu yawan gaske dazan iya kare kaina dasu, amma nabaka dama kayi wannan binciken da kanka. Sannan k'arin bayanin dazan maka shine, mak'iyane zagaye dakai, sannan kowanne akwai manufar sa a kanka, abinda yasa suka taru maka da yawa akwai k'iyayyar mahaifanka data dawo kanka a yanzu, wasu saboda tsoron ta6argazar dasuka aikatane basason kayi mulki ka yak'esu, wasu y'ay'ansu sukemawa, wasu iyayensu ne, wasu kuwa kansune, dukkuma akan inhar kahau mulki zaka iya canja komai da hukunta kowane ya sakasu wannan k'iyayyar a gareka, a yanzu dai kanada Avedance guda hud'u zuwa biyar a hannu, na farko sune wad'anda ka kama da yaran nan, yakamata kasan wanene ya saka su kafin kasan dalilin sasun, na biyu Harun, yakamata kasan miyasa yake tad'eka bayan ka yarda dashi Yakuma San airrinka, na Uku shine Saleem, dolene a wannan karon kasan wanene ya sakashi aikin tsaida CCTV cameras a waccan ranar, na hud'u shine SD minene had'insa da mahaifina, na biyar shine Fu'ad wanene ya sakashi kaimu birnin gayu a waccan ranar, sai Malam saminu driver Alhaji balala dan akwai abinda ya Sani tabbas, hakama farhat ku sake bata tsaro sosai, dan mahaifinta zai kawo kansa gareka cikin sauk'i saboda k'aunar dasuke mata, Sauran kuma zuwa nan gaba zan baka haske a kansu, wad'annan dai ka gaggauta sanin abinda suka Sani a cikin kwanaki biyunnan kacal, dan mak'iya bazasu zauna kallonka ba suma, sunacan suna had'a kayan yak'i. zanje na kwanta, saboda yakamata zuwa gobe mu fara shirye-shiryen komawa gida bisa al'adar haihuwar Fari, yau Munubiya tana can ma ita”. Ido kawai ya tsura min yakasa koda motsi, na d'auki Amaturrahman Na Goya, sannan Abdurrahman da Abdurraheem kuma a hannu nayi ficewata. Sauran bayani na k'ok'arin mahaifiyarsa Momma kuwa bazan fad'a masa yanzuba, sai komai ya lafa, saboda suna tattarene da sirrikan dasuka shafeni wad'anda bazan ta6a yarda ya sansuba................✍🏻 *Kudai k'ara hak'uri dani, nasan a zak'e kuke da sonjin Galadima ya fara caskale, komai a sannu-sannu ne, dama ba tufk'ar keda wahala ba warwarar, babu abinda yakai k'arshen Novel da saka ciwonkai irin k'arshe, musamman ma mai sark'ak'iya, idan kuka cigaba da hak'urin bina kamar yaune komai zai k'are, shiyyasa nakebi daki-daki yanda kuma zaku gamsu cikin sauk'i.* _lallai Comments naku nasakani nishad'i, musamman addu'oin Ku gareni ni da mahaifina😭, harma nakan Gaza sanin yanda zan nuna muku jin dad'ina, amma ina kallon kowa wlhy, saidai idan bana cikin group d'in kuwa, ALLAH yabar zuminci, ina yinku irin Trillion's d'innan, I love you all wujiga-wujiga wlhy🥰🥰🥰🥰😍😍😍😍😘😘😘😚😅🤝🏻🤝🏻👍🏻🤸🏻‍♀_. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻3⃣0⃣ ................Galadima daskarewa yay a zaune, gaba d'aya magudanar jininsa tana neman Gaza aiki, saboda jininsa a daskare yake, dai-dai da bugun zuciyarsa salon datake bugunta da banne a yanzu, lallai masu kiran mata masu k'arancin *TUNANI* a zahiri sune masu k'arancin tunanin, lallai mata suna suka Tara, akwai mata akwai mata maza, juye-juye yay tayi a gadon ya kasa ta6ukama kansa komai, barci ya k'auracema idonsa, d'aya bayan d'aya Brain nasa ke markad'a maganganun Munaya dalla-dalla, wani murmushi yasaki yayinda yakai hannunsa yana shafo kwantaccen sajensa zuwa gemu, dukkanin bincikensa akan dai-dai yake, saidai rashin tsoron Munaya da kaifin basirarta ya matuk'ar k'ayatar dashi, ya tashi zaune yana jawo laptop ya kunna, saiga su Munaya sun bayyana a itada yara da Samha a kan gado, saidai yanda ya lura ba barci takeba itama, Dan tana d'an girgiza k'afarta daga kwancen. tsayin wasu mintuna ya kashe tareda mik'ewa ya d'auro alwala, abin salla ya shimfid'a ya fara gabatar da nafila kamar yanda ya saba inhar yanada lafiya. ******************** Yau likitocin Abie dasu Momma suna cikin farin ciki, saboda k'afarsa ta dama sun wayi gari tana motsawa, bayan gwaje-gwaje suna tabbatar da canjin da aka kuma samu a dukkan halittun ga66ansa, yau daga shi har Momma harda kuka, tako rungumeshi cikin tsantsar farin ciki da godiyar ALLAH, jakadiya sai fita tayi jiki na rawa..... Galadima na tsaka da salla kira ya shigo wayarsa, koda ya idar saiya share, har yana masifa a ransa wane ke kiransa a wannan time d'in bayan yasan shi mai iyaline (🤣 kaga mai iyali😜👍🏻). Ganin dai baza'a barsa yaji da abinda ya damesa ba saiya d'auka a masife da nufin kashewa, kad'an ya rage ya aikata hakan sai yaga Ashe Momma ce, mugun zaro idanu yayi, jikinsa na rawa yay picking video call d'in, Momma ce ta bayyana tana sharar kwalla, har taune harshe yake wajen fad'in “Momma mike faruwa ne?”. Ganin ya rikice saita hau dariya da share kwalla tana masa bayani, ta matsa kusada Abie ta had'asu, yaukam dai Galadima harda k'ananun hawaye yayi Dan dad'i, gashi yau yaji muryar Abie d'insa tafito sosai ba laifi. Sunja lokaci suna waya, har kud'in wayar Momma ya k'are sannam suka hak'ura, baibi kiranba yacigaba da mik'a godiyarsa ga ALLAH. ranar dai zumbur akan abin sallah yayisa, sallar asubahi ma a d'aki yayi sannan ya samu ya kwanta, barci mai nauyi kuwa ya kwashesa. Da shirye-shirye Munaya ta tashi, dukkan abinda zasu buk'ata tagama tanadar musu itada yara, Samha dai tayi tagumi tamkar zatayi kuka. Bayan anma yara wanka Munaya ma tayi sai ta zauna yin break fast, suna d'an hira jefi-jefi da laraba dake ma y'an uku shiri cikin wasu kayan sanyi masu laushi. A kullum Munaya kan tsarkake sunan Ubangiji idan ta kalli yaranta, takanyi mamakin anya kuwa daga jikinta suka fito? idan ta tuna a yanda mahaifinsu ya Samar dasu takanyi murmushi da cizar lips (copy copy😜😂). Duk abinda takeyi laraba na lura da ita, Munaya na birgeta sosai, Dan idan tana wani abun takanyi tunani kodai Munaya jinin sarautace? Dan salonta da takunta tana kamada na mashahuran y'ay'an sarakuna masu aji da Jan aji, cikin hikima irin tasu ta manya tace, “Ranki ya dad'e ko Baban y'an uku yatashi? Naga bakije dubashiba, gashi tun d'azun naga ankawo Karin kumallo, kuma since shima sunkai NASA amma baya falo. Munaya tad'an Sosa k'eya tana murmushi, tace, “eh iya, ban saniba koya tashi, amma bara na lek'a na ganni”. “yauwa ko kefa ranki ya dad'e”. d'aukar k'aramin mayafi tai ta fita, sanye take cikin sket da riga na wani yadi mai kama da boyal Orange color, an masa kwalliyar surfani kad'an da stones da milk . Sai mayafinta siriri ya kasance milk shima, tayi k'yau sosai gashi tasha d'aurin zarah buhari😜. Tunda ta fito daga bedroom d'inta idon Galadima a kanta, fitowarsa kenan daga wanka sanye da bathrobe da k'aramin towel a hannu yana tsane ruwan kansa zuwa fuska da wuya, daina tsane ruwan yayi yatsaya kallonta ta cikin Computer d'in, harta shigo falonsa, tad'anyi kalle-kalle da lakatar center table d'in falon da d'an yatsa, da alama tana duba ko da dattine, idonsa yad'an lumshe yana lasar lips, yabar gaban Computer d'in zuwa ga mirror, zamansa babu dad'ewa tayi knocking k'ofar tare da sallama, kamar bayaso ya amsa mata, ko kad'an bata wani jisaba, Dan haka ta harari k'ofar sannan ta bud'e ta shigo. Ko motsi baiyiba daga inda yake, saima cigaba da shafa mansa dayayi, itama batareda ta kallesa ba ta wuce zuwa ga bed d'insa tana fad'in “yalla6ai barka da asuba”. Yanda tayi wani masifar basar dashi saiya d'an waigo ya kalleta, sa6anin da da yake kallonta ta cikin mirror. Zanin gadon ta cire hankalinta kwance, ta wuce ga wardrobe nashi ta d'akko wani tazo tana k'ok'arin shinfid'awa. Mik'ewa yay ya tako gareta. Jinsa akwai nayi a kaina, amma ban lura da sanda yabaro gaban mirror d'inba, k'amshin sabulun dayay wanka dashi da man days shafa duksun addabi hancina, na d'ago gaba d'aya na ina gyara mayafina domin ya rufemin k'irji da k'yau, saboda kayan babu laifi sun kamani, wajen yakuma cika sakamakon shayarwa. Dab dani yake a she, koda na mik'e sainayi kamar zan fad'a masa a jiki, nadai samu nad'an jaa baya ina tunzura baki, taku d'aya yayi yakuma matsoni, na matsa nima, shima ya matso, hardai muka kai k'arshen bango, kad'an ya rage na yandda Prime dake saman drowan gefen gadon, Wanda hoton Y'an uku ne yasa akayi ya ajiyeshi a wajen, na kalla ina gyara masa zama cikin d'an rankwafawa kad'an, hakkane yabama gyalen damar kuma zamewa, batareda na luraba na tsaya sosai, nad'an 6ata fusaka ina fad'in “yalla6ai lafiya kuwa?”. Luuu yay da idanu saikuma ya bud'e a kaina yana cizar lips, ganin ya tsurama waje d'aya ido a jikina saina kalli wajen, baki na bud'e nakama gyalen zan rufe k'irjina da sauri ina tura baki. Caraf ya rik'e hannun, zan saka d'ayanma shima ya rik'esa, sosai na had'e fuska idona na tara kwalla, kuma matsoni yayi sosai, ya rankwafo da kansa saitin k'irjina, rufe idona nayi ina k'ank'amesu sosai saboda tsoron mizaiyine haka?......... Bankai k'arshen tunanina ba naji saukar iska a wajen, a hankali na bud'e idona, sainaga Ashe gyalen yake hurawa da iskar bakinsa danya bud'e sosai, kunya ta kamani, dan rabin k'irjin duk abid'e yake, wuyan rigar ya cika girma. Wata muguwar girgiza nayi, had'eda shock a lokaci d'aya, saboda saukar nutsatstsiyar Sumbata danaji a wajen, babu shiri na maida idona na lumshe ina sauke ajiyar zuciya cikin shashsheka da nima bansan nayiba. Hakan ba k'aramin yamutsa jinin Galadima yayiba, ya d'ago yana matsoni jikinsa sosai da maida hannuna duka baya ya rik'e da hannu d'aya, na manne da jikinsa sosai. K'asa nayi da kaina saboda wata matsananciyar kunya data ratsani da mamakinsa, murmushi ya saki, Wanda tundaga zuciyarsa ya taho, Dan naji alamar hakan ta k'irjinsa, ya wani kuma maida muryarsa very slowly cikeda k'asaita yace, “yalla6iya dama kinada lafiya haka?”. Bansan na d'ago kai da idoba na kallesa, baki bud'e nace, “kamarya? Dama nace maka banida lafiya ne? ni kabarni nayi aikina inada abunyi”. ta k'are maganar da kauda kai gefe tana tura baki. Gira d'aya ya d'age sama, cikin ta6e baki yasa yatsu biyu ya maido fuskata Inda take, yace, “kin tabbatar kinada lafiya?”. Yay maganar yana d'aura yatsansa kan la66ana da zagayasu a hankali. Yanzunma tilas na lumshe ido, jikina harya fara tauma, zuciyata kam sai fat-fat take tamkar zata faso k'irji ta fito. Gangaro da yatsansa yafarayi daga saman bakina zuwa wuyana har yazo k'irijina. Bansan nafara kamo addu'a inayiba azuciyata, gashi na kasa bud'e idanu, muryata na rawa nace, “please yalla6ai k...ka...kabari”.. Uffan bai ceba, idonsa akan fuskarta yana murmushi da taunar lips, kuma bai bar abinda yakeba har saida ya dire saitin da zuciyata take, yace “ita wannan miyasata fargaba?”. Bud'e ido nayi a hankali dan naga miyake nufi? Na kallesa, ya nunamin k'irjina da ido, a d'arare na kalla inda yatsan nasa yake, na had'iye wani yawu dak'yar ina fad'in “babu komaifa, kaga yara zasu iya kuka ina nan fa”. “Uhmyim” yafad'a yana d'auke yatsansa daga saman k'irjina yana maidawa kan k'uguna, ya tura hannunsa cikin rigata cikeda wani salo, hannuna nafara yunk'urin kwacewa, saiya tsaya kawai yana kallona, saida nayi harna jigata kafin yayi wani munafikin murmushi, ya matso da k'uguna da k'arfi ya had'e da jikinsa, saida naji zafi na yamutsa fuska da cewa “Uhchhh! Yalla6ai ciwo”. “Da gaske?”. ‘yay maganar cikin matso da fuskarsa dab da tawa tamkar zai had'e bakinmu, idonsa cikin nawa yace, “kinsan mizan baki?”. Kaina Na girgiza masa kamar wata sokuwa. Hannunsa Yakuma turawa cikin rigata har zuwa gadon bayana, a hankali yace, “k'yauta”. “K'yauta kuma? Tami to?”. K'ala baice daniba ya juyani ta hanyar murza k'uguna ya maidani saitin gadon yana lankwasani a hankali, yayinda shikuma yake biyoni idonsa kan lips d'ina danake motsawa amma maganar ta gaza fita. Muna gab da kaiwa gadon ya saki hannayena ya tallafe bayana da hannunsa, d'ayan kuma yana rik'e da k'uguna har yanzun, ahaka muka fad'a saman gadon, saidai bai sakemin nauyinsaba sosai, koda ya fad'o jikina banji zafi mai tsananiba, yay min runfa da faffad'an k'irjinsa yana matso da face nashi daf da tawa. cikin wata iriyar murya mai sanyi da k'asaita yace, “bud'e ido ki gani”. Ban musaba na bud'esu, sai cikin mayun nasa da har yau launinsu yakeda sirkin jaa, duk yanda naso fiddawa na kasa, dan ya hanani wannan damar, saima wasu abubuwa danaga tamkar yana zubawa cikin idona, batareda na fargaba na shagala nima nabar yunk'urin janye nawa. Munkai tsawon mintuna a haka, saida ya tabbatar nagama zuwa hannunsa sannan ya d'ora tattausan lips d'insa akan nawa ya fara sarrafasu cikin tsantsar nuna yana tare da kewa da bege. Ni munaya naga ta kaina, bansan ya akayi galadima yaci galabar samun kainaba, lallai shid'in yanada wani baiwar iya sarrafa mace a yanda yaso, ya mantar dake wacece ke balle daga ina kika fito, yakan basar tamkarma baisan micece wata soyayya ba, duk kuma randa kikazo hannunsa zaki tabbatar yacika namiji, Dan asalin jinin Malam bahaushen Na yawo ajikinsa, dukda kasancewar wayayye kuma bai girma cikin k'abilarsa ba, yakan maida hankali a harkokinsa, randa kuma soyayyar ta motso yabata muhimmanci Na ban mamaki (Matan hausawa konayi k'ayya ba hakan mazan hausawa sukeba😂?) (Shiyyasa Muke cewa basu iya soyayya ba🤭🤣⛹🏻‍♀). Sosai na shiga bashi dukkan goyon baya harda saka hannayena na zagaye bayansa dasu........... 😨yaukuma su Oga Galadima an tina da sadaki😌🤭😂. Tafiya tafara nisan da naji yana neman sakin layi, a kasalance na rik'e hannunsa dake yawo a jikina, sannan na fara k'ok'arin janye fuskata daya koma bama kisses tako ina, sai gwama numfaahi yake yana sakin tagwayen ajiyar zuciya. ganin bazai bariba nasakar masa siririn kuka, ina fad'in, “yalla6ai jegofa m....mu...mukeyi”. Sai a lokacinne ya tsaya cak, amma yak'i d'agani, juyo da fuskata nayi na kallesa, ya sake sark'e idonsa da nawa, idanunsa sunkuma rinewa launin jaa sosai, wani murmushin takaici ya sakarmin, cikin magana da k'yar yace, “kina kukane danna mori sadakina?”.. Wannan magana tasa tamun nauyi, Dan haka na gagara bashi amsa, sai janye idona da nayi hawaye masu d'umi suka gangaro ta gefen kunnena. Gefena ya koma ya kwanta yana cizar lips da lumshe ido, yayinda hannunsa ke shafa kaina saboda tuni d'an kwalin ya zame. A haka yafara magana a hankali, “toke yanzu Yaya kenan? naga alamar auren Contract yakusa k'arewa, gashi ko rabin sadakina ban Moraba, zaki dawomin da kayanane ko yaya?”. Kai wannan Bawa ya shahara a fagen rainin wayo, nafad'a a zuciyata, a fili kuma sai nace, “nima sai'a biyani d'aukar ciki da nak'uda, da shayarwa ai, tunda babusu a yarjejeniyar auren”. Yanda nayi maganar ina yamutse fusaka da murgud'a baki saiya shagala da kallon la66anta, hannu yasaka ya tallafo fuskarta yajuyo da ita sosai inda tashi take, dukda idonta a rufe suke, “kifad'i ko nawane sai a biyaki ai, nikuma ba kud'in Dana bayar nake buk'ata ba”. Na bud'e ido baki bud'e, “to mi kake buk'ata? Naga kud'i ka bada kuma kud'i ya kamata a baka”. Cikin ta6e baki yace, “farashina ya wuce haka”. Nina bakin na ta6e nace, “Niba arhar banza bace”. Nayi maganar ina yunk'urawa da tashi zaune, da kallo ya bini, saida na ziro k'afafuna k'asa sannan nakuma fad'in “mun gama sahirinmu”. Shiru yamin tamkar bazai tankaba, harma na juyo na kallesa, idonsa a rufe suke yayi filo da hannayensa, d'auke idona nayi ina gyara rigata. Yace, “zuwa ina kenan?”. Nace, “gidanmu”. Tashi yay ya sauka daga gadon duka yana nufar wardrobe, saida ya bud'e yana kallon kayansa sannan yace, “mizai hana kibari ki k'arasa aikinki kawai saiki tafi gaba d'aya”. Na murmusa ina mik'ewa tsaye nima, na koma jikin mirror na jingina ina hard'e hannayena a k'irji, idona akansa nace, “aini nagama aikina, Dan nabaka dukkan sirrin dake raina”. Yana ciro wasu bak'ak'en wando da Riga yace, “zadai ki gamane yarinya, Abin cikin kwan bazasu gusa a kusa daniba”. “Humm” nafad'a cikin takaici, nace, “mizai hana ka yanke dukkan alak'a, Dan nima iyayena na buk'atar ganina a kusa dasu”. Murmushi yayi yana juyowa hannunsa d'auke da kayan daya za6o, kallo d'aya yamin ya janye ido, “mikikeci na baka na zuba babie, indai an gama yak'in ai zata yanke”. “nikuma bana buk'atar ganin k'arshen, in ank'i cikin sauk'i zan bud'e komai kowa ya sani”. Murmushi yay mai sauti, har fararen hak'oransa na bayyana, ya kwance igiyar rigar wankar babu kunya ko shakkar ganina, kauda idona nayi daga inda yake, yafara saka kayansa, cikeda izza yace, “wace k'arfin gwiwa gareki na samun wannan damar?”. “Court, tabbas zan maka ka a Court, sai a kar6a min ai”. “kinada abin dariya kwarai da gaske, a mutum dubbunai dasuka shaida na biya sadaki sannan na d'auka, mutum d'ayane yasan sirrin ba haka bane, bayan wannan hujjar kinada watane?”. Dariya nayi irinta tsantsar rainin hankali, harya d'ago daga d'aura belt d'in da yakeyi ya kalleni sannan ya janye, zama nayi a stool mirror, na d'ora k'afa d'aya kan d'aya ina girgizawa, “yalla6ai kenan, a tunaninka zaka iya cin bulus ne?”. Murmushi kawai yayi bai sake tankawa ba, Dan ya kula ciwon kai take Neman saka masa, ya zauna bakin gadon yana saka sock's da takalmi, yayinda Munaya taketa cika da batsewar sharetan da yayi. rigar jacket d'insa milk color ya d'ora bisa bak'ak'en kayan, komai nasa ya kasance bak'i, jacket d'ince kawai milk, ya matsa gaban mirror kusada ita yana gyara sajensa da fesa mayen turarensa. Saida ya gama dukkan uzirinsa kafin yazo gabana ya tsaya hannayesa duka zube a cikin aljihu. Dan k'yau yayi k'yau kam, amma saina kauda kai gefe ina ta6e baki, irin bakayi d'innanba. Shima bakin ya ta6e yana rankwafowa kaina har inajin hucin numfaahinsa, “karki damu mai yabawar tana nan tafe lokaci kusa, matar Sameer sarauniyarsa kinji yalla6iya”. Cikin azama na mik'e, yay saurin ja da baya, Dan daya tsaya saina buga masa kaina wlhy. Hanyar fita na nufa ina fad'in “idan kana buk'atar y'ay'anka zaka iya bina gidanmu ka kar6o abinka”. Da kallo yabi bayanta kawai yana ta6e baki, akan la66ansa yace “iya tsiwa”. Agogonsa ya d'auka bak'i ya d'aura, sannan yazuba wayoyinsa a aljihu tareda saka eyeglasses mai duhu a idonsa, ya 6oye tsananin jaa da sukayi, a falo ya iske tea a cup an had'a yanata turiri, zama yay yana lumshe idanu, yakan rasa Munaya wace irin macece ita? So salon nata akwai tsagwaron k'ayatarwa, Crossing k'afarsa yayi yana shan tea d'in a hankali, yasha kusan rabin cup ya ajiye yana mik'ewa da kallon agogonsa yanajan k'aramin tsaki. sashen Munaya ya nufa, bayin daketa gyare-gyare suka zube suna gaidashi, hannu ya d'aga musu kawai batare da yace k'ala ba, cikin takunnan nasa na k'asaita da izza yake tafiya, bayinnan sai satar kallonsa suke, da sallama ciki-ciki ya shigo d'aki, Laraba tai saurin risinawa tana gaisheni, ya amsa batareda yako kalleta ba, ficewa tayi da hanzarinta, Samha ma ta gaidashi. Zama yay a bakin gadon idonsa akan akwatina da Munaya ta had'a, ya janye ya maida kan yaran yana fad'in “ku shirya gobe zaku koma?”. Cikin d'oki Samha tace, “Uncle Sam harda Aunty gimbiya?”.. Cire glasses d'insa yayi ya maka mata wani kallon daya saka hanjin cikinta mitsawa, yace “tare kuka zone?”. Da k'yar ta had'iye yawu tana girgiza masa kai. Da yatsa ya nuna mata k'ofar fita, jiki na rawa ta ajiye Amaturrahman tafice tana tuttura baki da share kwallan shagwa6a. Ya lumahe ido yana jan tsaki, Munaya dai na zaune tana had'a wasu y'an kaya da suka rage a k'aramar bag, ko kallo basu isheta ba. Rankwafawa yay duk ya sumbaci kumatun yaran, sannan ya kalleta fuska babu alamun yasan dariya yace, “wannan kayanfa?”. Duk da na tsorata da yanayinsa, hakan bai hanani dakewa ba, cike da jan aji nace, “Na tafiya”. Uffan baice daniba ya mik'e, kansa tsaye ya nufi k'ofa, nikuma nabisa da kallo harya fice. Wasu hawaye danake rik'ewa tun lokacin dana baro d'akinsa suka samu damar zirarowa, hannu nasaka na sharesu ina zuge zip d'in bag d'in. Waya na d'auka na kira Momma, na gaisheta cikeda ladabi, albishird'in cigaban jikin Abie da aka samu ta sanarmin, tsantsar farinciki ya sake kamani, nace insha ALLAH su Samha ma zasu taho da wasu magungunan. godiya tamin da sake sakamin albarka, ta tambayeni ya mukayi dashi?. Na sanar mata yace baza'a jemai ko ina da yaraba. Murmushi tayi mai sauti har ina jiyota. “karki damu d'iyata. Da Kansa ma zai kaiku”. Na amsa mata da to kawai, Dan banga alamar Galadima zai tankwaru ta cikin sauk'iba akan tafiya wanka d'innan. *********** Tunda ya fito hadimansa keta kwasar gaisuwa damasa Yaya jiki, hannu kawai yake iya d'aga musu fuskarsa babu walwala, sarkin mota da dogaran dakan bisa yayin fita suka taso da hanzarinsu, bud'e masa mota akayi ya shiga. Saida Sarkin Mota ya tada motar sannan yace, “ranka ya dad'e ina muka nufa?”. Banza ya masa kamar bazai tankaba, sai zuwa can yad'an nisa yana bud'e ido, “mu fara Shiga wajen mai martaba”. “Angama ranka ya dad'e”. Sarkin mota ya fad'a cikeda girmamawa. Bai fita a motarba, sarkin mota ne yafita domin nema masa iso, amma sai jakadiya tace, “ai takawa tunda safe suka fita shida su Masu da baraya. Sarkin mota yazo ya sanarma Galadima, baice komaiba sai kansa daya jinjina kawai. Daga nan basu zame ko inaba sai gidanda su Muftahu suka kai yarannan. Muftahu da kansa ya bud'e musu k'ofa suka shiga, aka bud'ema Galadima ya fito, tafiya yake a nutse cikeda k'asaitar masu mulki da tashen k'uruciya, Muftahu ya tako a hanzarce garesa, hannu yabasa sukayi musabaha, sannan suka cigaba da tafiya cikin gidan a jere, fuskarnan babu walwala yace, “ya kuke ciki dasu?”.. Muftahu yad'an nisa yana bud'e masa k'ofar shiga falon dansun k'araso, “Ranka ya dad'e bamu tambayesu komaiba, Dan wannan ba Hurumin mu baneba ai”. Galadima baice komaiba, ya zauna kujera mai zaman mutum d'aga yana d'ora k'afa d'aya kan d'aya. Muftahu bai zauna ba saida ya d'akko glass cup da kwalin Hollandia ya ajiye gaban Galadima. Galadima dake danna waya yad'an d'ago ido ya kallesa ta cikin glasses, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru ya maida kansa ga wayar. Girgiza kai kawai Muftahu yayi, Dan yasan magana yakesonyi amma yaza6i yayi shiru daya bud'e bakin. yana tausayama Munaya wlhy, “Ranka ya dad'e su zone?”. dan yasan bai wuce abinda yake son cewa kenanba. Ilai kuwa sai Galadima ya jinjina kai yana nuna yatsansa d'aya alamar mutum 1 yakeso. Nanma dai Muftahu kan ya girgiza kawai sannan ya mik'e. Mintuna uku kacal saigashi da mutum d'aya a cikinsu. har yanzu kuma idon Galadima nakan phone nashi. Saurayi da bazai wuce shekaru 30 zuwa sama a duniya ya durk'usa gaban Galadima kamar yanda Muftahu ya umarcesa, kwarjinin Galadima da cikar haibarsa da tsare gida duksun rikita gayen, bakinsa na rawa yace, “barka da safiya ranka ya dad'e”. K'ala baice dashiba, kusan mintuna biyu ya ajiye wayar yamasa kallon tsaf sannan ya janye idonsa, kansa ya jingina da kujera ya lumshe idanu, hannayensa duk suna bisa hannun kujerar, cikin maganar nan tasa mai kama da anmasa dole yace, “wanene kai? miya kaika gangancin shiga hurumina?”. Ba k'aramin tsuma da birkita muryar Galadima ta saka guy d'inba, haka kawai sautin muryar Galadima dabata da r a cikin kalami ya rikita guy d'in, murya na rawa yace, “Ranka ya dad'e sunana Shazali, kuma wlhy bansan komaiba, nidai kawai anzo an bamu aikine”. Halbi Muftahu yakai masa yana fad'in “k'arya kakeyi”. “Wlhy da gaske nakeyi”. Shazali yafad'a cikin mak'yark'yata. d'agowa Galadima yayi zaune sosai, yace, “kozan iya sanin wanene yabaku aikin?”. “Bansan sunanta ba Ranka ya dad'e, amma zan iya ganeta”. Kallon Muftahu Galadima yayi, Muftahu daya san abinda yake nufi ya jawo laptop yana ajiyewa gaban Galadima. Zama ya gyara, cikin kwarewa yafara sarrafa System d'in yana cizar lips kad'an-kad'an, wannan salo na yarima yana burge Shazali, aransa yana jinjina mulki mai dad'i kenan, haka kawai k'aunar Galadima ta shigesa, kuma yayi alk'awarin taimakonsa cikin sauk'i insha ALLAH....... Tunaninsa ya katse lokacin da Galadima ya turo masa laptop d'in. Kallonsa yad'anyi Dan baisan mizaiyi da itaba. d'auke kai Galadima yayi alamar bazai yi magana ba. Muftahu yace, “ka duba idan akwaita anan”. Laptop d'in Shazali ya ida jawowa gabansa, hotunane suka bayyana da yawa. Muftahu yamatso yana masa zooming nasu one by one. Nuren yafito daga wani d'aki yana mik'a, da mamaki yake kallon Galadima dashima shi yake kallo, “brother kaine?”. Kai Galadima ya girgiza masa alamar a'a. Nuren ya murmusa yana tahowa cikin falon, hannu yabama Galadima sukayi musabaha, yana tambayarsa yaya jiki?. Akan la66a ya amsa da “Alhmdllh”. Nuren yace, “ina yarana?”. Da hannu yamasa nuni da lfy. Kular da Nuren yayi yau k'asaitar a kusa take saiya barsa ya mik'e, Coffee ya had'o yadawo ya zauna yana kallon abinda su Muftahu sukeji. Shikam Galadima yayi shiru yana tunano yanayinsu da Munaya na d'azun, yana da buk'ata mai tsanani, saidai yakan danne saboda jarumta, musamman idan ya tuna matsayin auren nasu, ko a baya saboda yanayin data shigane ya sakashi yin yadda yaso da ita, Dan hak'k'insa ne ya taimaketa a lokacin kodan buk'atar tazame mata lalurar cikinsa, yanzu kam dolene yanemo mafita ko matar aur.......... Tunaninsa ya katse lokacin da Shazali ke fad'in “itace wannan yalla6ai”. Daga Muftahu har Nuren kallon picture d'in suka tsaya yi, sannan duk suka kalli Galadima da shima idonsa ke Kansu. Nuren ya d'auki laptop d'in ya mik'a masa, shiru Galadima yay yana kallon hoton, Matar Abie ce ta biyu, wadda yata6a gani a wayar Harun, yay wani miskilin murmushi yana yana kallon Shazali, saikuma ya janye idonsa batare da yace uffanba. Shazali ya gyara zama yana fad'in “bayan ita kuma sai aka had'amu da wannan matan daga masarauta, sukuma sunce Uwar gidan sarkice ta sakasu”. Nuren yace, “uwargidan Sarki kuma? to tayaya tasan kud'in ga abinda zakuyi?”. “wlhy ban saniba nima ranka ya dad'e, abinda na Sani kawai a ranar wlimar kafin mu shigo hall d'in aka taremu a hanya, shine wani dogari ya shigo motarmu, da farko mun taso masa harda fiddo wuk'ak'e, saishi kuma ya nuna mana bindiga, hakanne ya sakamu nutsuwa, yace, yasan abinda zamujeyi ai, dan haka idan munason mu tsira da ranmu mu sauraresa da k'yau, shima aiki zai bamu. Zai had'amu da bayi biyu mata dazasu taimakemu mu sace yaran, bayan mun gama akwai kaso mai tsoka, sannan zai fad'a mana wani sirri, mahaifin yaran yayi shirin canjasu da y'ay'an babyn roba dan haka karmu sake mu d'auki yaran da za'a bama wasu yara, mu d'auki na cikin gado daza'a sakasu a wajen taron, sune zasu zamo na gaskiya, mak'udan kud'in daya bamune suka samu amincewa da gaggawa, Yakuma sanar mana aikin uwargidan sarkine, idan har mukayi kuskuren wani yasani dagamu har ahalinmu sai sun shafe labarinmu a doron k'asa”. Daga Muftahu har Nuren kallon Galadima suke da mamakin Brain nashi, hakan suka shirya, amma daga baya sai sukaga ya canja yabada yaran da gaske, sunyi mamaki sosai, amma bai basu fuskar tambayarsa ba a time d'in. Yay musu alamar miye suke wani kallonsa. Salute d'insa sukayi su duka, ya kauda kansa kawai yana ta6e baki. Sun kuma tabbatar da akwai sirrika da yawa da Galadima ya Sani, akwai yana basarwane saboda jiran lokaci. Da hannu yamasu Nunin Shazali yatashi yaje. Bayan tafiyar Shazali ya kallesu yana sauke ajiyar zuciya da gyara zamansa, ya d'auki kwalin hollandia yazuba a cup, Muftahu da Nuren dai na kallonsa, saida yafara sha da kallon agogon hannunsa sannan yace, “Zanje India gobe idan ALLAH ya kaimu, akwai ayyukan dazan tattara na kwanaki uku, sannan na d'auki Hutu a wajen aiki, dukda muna shirye-shiryen fidda kaya na shekara mai zuwa, a Daren yau Harun zaisan matsayinsa, Dan tuni nagama da matsalarsa dama, wannan ranar nake jira, so Nuren ka bincikamin inda matarnan take zaune a yanzu, Dan ina dawowa zan shiga aikine sosai, matsalar Harun da ita da Sarauniya kowanne akwai manufa, su nasu wasan yarane a wajena. Erfan shine yajema Munaya a matsayin Fu'aad, yanzu na fahimci sune suka saka aka buga waccan jaridar, amma da saka hannun wasu a gefe........” Muftahu yay saurin cewa “yi hak'uri ranka ya dad'e zan katseka, sai yanzu wani Abu yazomin a rai, wato ranar salla a filin idi, kasan Erfaan yana tare damu, anya kuwa ba a wannan time d'in ya ganku kaida gimbiya ba, lokacin da kukayi karo, wata k'il shikuma yayi tunanin alak'a Ce a tsakaninku?”. Murmushi Galadima yayi yana lumshe ido, “ni kaina ina tunanin haka, saidai akwai wani Abu bayan wanna, dan haka sarakuna uku sun shigo cikin aikina”. Da mamaki Muftahu da Nuren sukace sarakuna kuma?. K'ala baice da suba ya mik'e tsaye, ya kalli agogon dake tsintsiyar hannunsa sannan ya kallesu, “gobe da safe Alhaji Shehu Darma zaije taron k'arama juna sani a jihar Katsina, lallai bana buk'atar yama k'arasa”. Kusan a tare sukace Alhaji Shehu Darma kuma?. Ficewarsa yayi batareda yabasu amsaba balle su sami k'arin bayani. baki bud'e Nuren da Muftahu suka kalli juna, Muftahu yace, “shikuma miye nasa to?”. Cikin jimami Nuren yace, “nima abinda nake son Sani kenan, mutumin da tunda mijin aunty Mimi ya rasu yake fad'i tashi a kanta da yaranta, danma tak'i amincewa ne da aurenta zaiyi, anya kuwa shi yake nufi kodai wanine mai irin sunansa?”. Jiki a sanyaye Muftahu ya yarfar da hannu alamar bai saniba shima. danshi lamarin Galadima yafara bashi tsoro, mutum kamar wani tsohon aljani. Shikam koda yabar wajensu wani office yace Sarkin mota ya kaisa, yakai tsawon lokacin a wajen tareda wani mutum dabazai gaza shekaru 56 ba a duniya, bansan mi suka tattauna ba, dan ba'a bani damar jinba. A wajen yay sallar azhur har la'asar sannan yayo masa rakkiya wajen Motocinsa, saida yaga fitarsu sannan yakoma Office d'in. Daga nan masarauta suka nufa, dan Galadima a matuk'ar gajiye yake, Ya iske sashensa fes an gyara, ko ina yana tashin k'amshi tamkar yadda yake buk'ata, kayansa yacire ya watso ruwa, bai nemi kowa baya ya zauna a falo yana aiki a System, dukda yaga abincin da aka ajiye masa baiko bud'eba balle tunanin cinsa, Yakuma san Aunty Mimi ce zata saka a kawo. Yana tsaka da aikin Sauban ya shigo, bai kallesaba koda ya gaidashi, yadai Amsa. Sauban yace, “yaa Sam tafiyar safe zamuyine goben?”.. Ido Galadima yad'an d'ago ya kallesa, ya maida kansa ga laptop d'in yana fad'in, “Kwana 3 zamuyi ni da kai mu dawo, komanka na gameda bautar k'asa yagama kammaluwa”. Kamar Sauban zai sanya kuka yace, “Amma Yaa Sam su Momma sai abarsu babu kowa?”. “kafin ka girma dawa suke zaune?, Sauban ka kiyayeni, karka bari na fusata akanka, tashi bani waje”. Sauban ya mik'e zuciyarsa na zafi, harzai fita Galadima yace, “zonan”. Dawowa yay yana mirgina kai, batareda Galadima ya kallesa ba yace, kar6a wannan, kaje ka sakashi jikin rigar Abdurrahman ko Amaturrahman ka d'auki Wanda ka samawa d'in kaje sashen Ummu Amaan (gimbiya Zulfa) dashi”. Sauban baice komaiba ya kar6a abinda yabashi mai kama da ma6alli ya fita, ya iske Munaya na barci, yaran kuma na tare da Khaleel dake ta fama jagwalgwalasu, Abdurrahman ya d'auka ya sakamawa ya nad'eshi a showal ya fita...... Nikam wannan gangancin na Galadima ya isheni😨🙆🏽. Bansake jin miya faruba dan banbi Sauban ba nikam, ina tsoron ganin abinda zai hanani barci😌. __________________________ Misalin 8:30 na dare Galadima ke shiri bayan ya dawo daga sallar isha'i, yagama tsaf cikin k'ananun kaya da jacket d'insa wadda takai masa har gwiwa, ya saka safa har a hannunsa, cikin takunnan nasa na gwarzantaka ya fito, sashen Munaya ya nufa, sukaci karo a k'ofar d'aki zata fito a rikice, sauri tareta yayi ta fad'o jikinsa saboda kad'an yarage ta fad'i, k'amshin turarensa ya sakata shaida shine, ta share hawayenta tana kallonsa a rikice, shima kallonta yakeyi, Muryarta na rawa saboda kuka tace, “yalla6ai Abdurrahman sai kuka yakeyi, jikinsa ya d'auki zafi”. Baice komaiba ya kama hannunta suka koma cikin d'akin, laraba da aunty Mimi na zaune, aunty Mimi tana zarema Abdurrahman kayan jikinsa za'a watsa masa ruwan d'umi kozaiyi shiru. Zama yayi ya kar6e sa daga hannun Aunty mimi, ya fiddo wani kwali k'arami daga aljihun jacket d'insa ya bud'e, k'aramar kwalbar dake cikeda magani ya fiddo, ya d'iba maganin cikin tsinken da ake bama yara magani ya zubama yaran a bak'i, dak'yar ya shanyeshi. Sudai sunyi jugum-jugum suna kallonsa. Yunk'urin amai da yaron keyi yasaka Galadima d'agashi daga jikinsa dan kar yay masa, baimayi amanba, hakanne yasaka Galadima sauke ajiyar zuciya ya mannashi da k'irjinsa yana hura cikin kunnen yaron a hankali. Tun yana kukan kad'an-kad'an ya koma ajiyar zuciya, sai gashi yayi barci. Kwantar dashi yayi kusada y'an uwansa ya lullu6esa. Ya kalli aunty Mimi yana mik'ewa, “insha ALLAH zai sauka zaza6in”.. Yanda Aunty Mimi kebinsa da kallon tuhuma saiya janye idonsa yakama hanyar fita, da sauri tamik'e tabi bayansa a fusace. Dan Sauban ya sanar mata Galadima ya sashi kai yaron sashen mai martaba d'azun. “Dakata Sameer”. Cak ya tsaya yanajan hular rigar bisa kansa, amma bai juyoba. “Sameer wai mike damun kankane haka? da zaka ringa wasa da rayuwar yaranka da kanka?”. Lips d'insa ya ciza, ya juyo yana kallonta, amma ita bata ganin idanunsa saboda hular ta rufe, murmushin takaici yayi, yace, “Ni ba wasa da rayuwarsu nakeba aunty Mimi, komai kikaga nayi nasan abinda nakeyi, zuwa nangaba kad'an kuma zaku fahimci komai”. “ALLAH yasa to, amma ni yanzu na zone muyi maganar komawar Munaya gida kafin mu wuce goben, tunda jirgin rana zamubi”. Agogon hannunsa ya kalla, yace, “yanzu kam inada uzirin fita?”. “fita? Inakuma zakaje a wannan daren?”. Batareda ya tanka mataba yajuya yakama hanyar fita, saida yaje bakin k'ofa sannan yace, “Farauta”. yay ficewarsa. Kasa motsi aunty Mimi tayi a wajen, sai maimaita Sunan Galadima kawai takeyi akan la66anta. ****** Tacan baya yabi shikam, hanyar akwai k'arancin mutane sosai, yana zuwa ta wani waje yagamu da wani Wanda ke sanye da irin kayan hadiman masarautar, rissinawa yay yabashi keys d'in mota. ya kar6a batareda sunma juna maganaba ya wuce. Can sashen su Harun naga ya nufa, dukda tazarar dake tsakaninsu baiji tafiyarba, motar dake fake a wajen ya bud'e ya shiga ya zauna, zamansa da mintuna uku Harun yafito ad'an hanzarce, motar yabud'e seat d'in baya ya shiga ya zauna, cikin bada Umarni yace, lawandi muje, kasan d'an bala'innan yanada securitys dake kaimasa rahoto”. Murmuahin gefen baki Galadima yayi yatada motar yafice daga masarautar................✍🏻 “Hummmm! Reader's harna sauke numfashi, babbar magana, yau dai ga Galadima ga Harun, sauran abinda zai faru kuma sai a buk 3 na raina kama”. Miya faru da Abdurrahman lokacin da Sauban ya kaisa sashen gimbiya zulfah ne🤔? Yaya batun kama SD?, wad'anne sarakuna ne Galadima yake zargi? Kodai dama can Galadima yasan wanene Harun yabashi damane kawai?🤔, Yaya batun warkewar Abie da Auren Contract tsakanin Galadima da Munaya?, mi suke shiryawa itada Momma da suka damu da zuwanta wankan gida? Ko Galadima zai amince?”. Yaya batun gano asalin innarsu Munaya? Da ita Munayar ta d'auki alwashi?. Tofa wannan amsar dai duk zatazo a littafi na 3 kuma na k'arshe da izinin ubangiji, dukkan wasu tambayoyinku amsarku na cikinsa, zan had'a muku da albishirin zan dingayi a weekend rana 1, kodai asabar ko lahadi, kowacce rana nasamu dama aciki, dan buk 3 inason kammalashi ne a gaggauce saboda uzirin danake dashi insha ALLAH. Ngd sosai da had'in kan da kuke bani, muje zuwa my guys⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀🥰🥰🥰🥰🥰🥰😍😍😍😍😍😍❤❤❤. Barkanku da juma'a🙋🏻. Musha weekend lafiya⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* __________________________ *_Kai jama'a yau dai kun Sani typing dole saboda munafurcin y'an bani Na iya, wannan karon kuma kurasa k'ullin da zakuyi sai akan Uwa da 'Diya?, nikam yau koda mamana (mamu gee) kwaikwayar RAINA KAMA tayi to wlhy birgeni zatayi, ai baiwace ma wani yayi Abu kabishi daki-daki kana kwaikwayo. Irin wannan shirmen naku baya cikin kan Bily, ba mamu gee ba koda watace aka jingina da hakan bazanji komaiba wlhy, sannanma nifa abinda yabani mamaki a writeup d'in da mamana tayi bata ambaci sunan RAINA KAMA ba aciki ko wani littafi daban, to tayaya y'an bani Na iya da tsugunne-tsugunne su anasu writeup d'in suka saka sunan RAINA KAMA? (Wlhy halin wasu daga cikin writers namu ko kad'an bashida k'yau, neman sunane kokuwa son asanine niban saniba🤦🏻‍♀)._* _Reader's kuma da naku, sometimes bakunanku basuda linzami, irin wannan abubuwan kune ke fara tsirarsu saisuzo kuma su buwayeku, Ku ke karanta RAINA KAMA DA TARAYYA Ku kusan banbancin abinda ke cikin kowanne, amma dayake Ku irin wannan dama shine farin cikinku saikuyita k'irk'irar abinda dolene daga k'arshe saiya zama rikici, to nikam zan sanar muku, awanan karon sai had'in naku baiyiba, Dan MAMU GEE DA BILYN ABDUL duk Abu d'ayane, daga tarayya har Raina kama buks d'inmu ne, mu muke rubuta abunmu, babu wata munafukar writer ko reader da mukayi shawara da ita kafin mu d'aura alk'alaminmu a takarda, masu had'a husuma kuma sai kusha fetur Ku had'iyi ashana kuyi bombing d'in kanku, ina dai shikenan ko?🙅🏻_. *Daga k'arshe inamai muku nasiha da kuji tsoron ALLAH, wlhy bashin naira 10 kacal yana hana bawa kwanciyar kabari, karo tsakanin rago da rago kawai akwai hisabi tsakaninsu, aranar kiyama bayan an tsaya hisabi duk Wanda kasani koya sanka saika Ganshi kakuma ganeshi, bawai kaitsaye za tantanceka akaika wuta ko aljanna ba, wlhy sai an tsidaka, ancire hak'in mutane a kanka, ka zagi wane babu hak'k'insa, ka harari wane, kama wane zind'e, ka cinye kud'in wane, ka had'a fad'a tsakanin wane, ka 6ata sunan wane, ka cuci makwafcin, ka...ka...ka...da yawan gaske, duk wani cin amana ko zalunci dakama wani inhar bai yafe makaba a wannan ranar sai an cire masa hak'insa a cikin ayyukanka, (Dan sune kad'ai guzirinka) komai tarin aikin alkairin daka tara inhar kanada irin wad'annan bashishshikan d'aya bayan d'aya sai an zaresu daga gareka, koda dabba da kafiri ka zalunta kuwa, idan dama bakada komai, sai ayita kwashe nasu zunubai ana lafta maka, sai angama tas, kabiya an biyaka saikuma a gwada ayyukanka a kan mizani, miyarage kuma? Saika koma gefe jiran sakamako. Wlhy y'an uwa babu babban tashin hankali irin kar6ar sakamako, a wannan lokacin uba baya gane d'ansa, y'a bata gane uwarta, miji baya gane matarsa saboda tsantsar tashin hankalin da ake ciki, da wane hannu xaka amsa, ina ne zaizama mazauni Na dindindin, duk baka saniba, haba y'ar uwata, kinada wannan babban aiki a gabanki amma kika shagala wajen had'a husuma irin ta social media wadda bansanki ba, baki sanniba, maybe ma har Abadan bazamu ta6a sanin junanmu ba, muji tsoron ALLAH wlhy, yakamata irin wannan abubuwan su tsaya hakanan, daga ni har mamana badan Neman suna mukeba, domin Isar da sak'o mukeyi a cikin tarayya da raina kama, burinmu kuma ko mutum d'aya ya amfanu da manufarmu ya wadatar, bawai tarin masu karantawa ba, ni miyasa babu Wanda yata6a tarata yacemin tarayya copy d'in raina kama ne? to Ku kama kanku please, kodan tsoron ALLAH.* _My Sweet mah-mah mamu gee wannan page d'in sadaukarwane a gareki, kiyi yadda kikeso dashi nabaki, ALLAH yabarmu tare, I love you irin trillions d'innan, kisamun albarka nakuma zama gagara badau😁😘._ Bilyn Abdull & Mamu gee RAINA KAMA ne mu, sannan munyi TARAYYA NE akan Isar da sak'o mai muhimmanci, mabiyanmu Na gaskiya a KAFTA kawai⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀😂👍🏻. HARUN da GALADIMA kuma Ku KAFTA naku wasan🤣🤣🤣🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀✍🏻😜. __________________________ ~Book 3~ 👉🏻1⃣➖2⃣ ...............Saida suka fara tafiya sai Harun yafara jin tamkar k'amshin turaren Galadima yakeji, mamaki ya kamasa, ya kalli gaban motar yana fad'in “lawwali nikam kaji minakeji kuwa? k'amshin Sameer fa”. Murmushi Galadima yayi, baice komaiba sai “Uhmm”. Hakan yakuma d'aure kan Harun, kamar zai sake magana saiya fasa, ya d'auki wayarsa domin son kira yaji ina Galadima, yasan Abu dolene ke fiddashi da daddare daga masarauta, amma sai kira ya shigo a wayarsa, k'aramin tsaki yayi Dan ba'a ko'ina yake d'aga wayaba, ya yarda da lawwali drivern babansa waziri amma bakomai yake barin ya saniba, ganinfa an damesa da kiran saiya d'aga. Da sauri ya janye wayar a kunnensa yana lek'o kansa gaban motar danya tabbatar. shin ina tunaninsa ya tafi dahar ya iya gaza banbance lawwali da Sameer?. yace “Sameer!”. Galadima dake tuk'insa hankali kwance yana kuma sauraren wayar Harun ta abinda yasa akunne, saboda ya saita duk wayar dazata shiga ta Fita a war Harun saiya shigo wayarsa shima kota fita yace, “Uhmyim”. A tsorace Harun yakoma baya ya bigi seat da k'arfi, babu abinda zuciyarsa keyi sai dukan 100-100, wayarsa ya jawo jiki Na rawa yafara k'ok'arin kiran wani. Galadima yay murmushi, cike da izzar k'asaita yace, “bar wahal da kanka my dear friend, duk wata waya dazaka kira a yanzu wayata zata shiga”. Harun yay jifa da wayarsa a kujera jiki yana rawa, batare da wani tunaniba ya mik'e kawai ya shak'e Galadima, da hannu d'aya Galadima yake driving, hannu d'aya kuma yana k'ok'arin kare kansa daga shak'ar da Harun ya masa. Da k'yar yasamu ya gangara gefen titi, yasaka hannunsa d'aya ya bigi gefen cikin Harun daya samu damar shak'esa da k'yau, Dan numfashin sa harya fara fita afisge. Dukan cikinsa da Galadima yayi yasakashi sakinsa da sauri, Galadima ya juya yakuma naushin bakin Harun saiga jini, dama bai gama dawowa hayyacinsa ba daga dukan cikinsa da yayi. Harun ya fad'a saman kujera yana rik'e ciki da shafar hancinsa dayaji yana yoyo, kallon hannunsa yayi saiyaga jini, ya zaro ido cikin matuk'ar mamakin shi Sameer ya fasama baki, yo ko danbe zasuyi ai babu abin zai d'auka a jikinsa, (Dan shima Harun d'infa ba bayaba). Galadima daketa huci ya dafe sitiyari da kife kansa ya kuma tada motar a harzuk'e ya fara tafiya cikin tsananin gudu. Cikin hakki da fidda numfashi a wahalce Harun yace “Sameer n..n..ni ka daka? harda fidda jini?”. Banza Galadima yamasa yacigaba da tuk'insa, Harun ya kuma yunk'urawa zai tashi amma saiya kasa, saboda ba k'aramin duka Galadima ya masa a gefen cikiba, wajen ya k'ulle, dole ya koma ya kwanta yana cije baki da matse ido, hannunsa rik'e da wajen har yanzu. Suna isa inda ya nufa yay horn, saiga Nuren da kansa yazo ya bud'e masa k'ofa, a fusace ya shiga gidan, shi Nuren ma har yana tsorata. Yana tsaida motar ko kashewa baiyiba yabud'e ya fito a harzuk'e, inda Harun yake ya bud'e ya jawoshi, yakuma kai masa naushi, shima ya kai masa dukda azabarda cikinsa ke masa. Nuren da Muftahu sun iso wajen a hanzarce, Dan ganin danbe Na Neman hark'ewa tsakanin aminai guda biyu, Nuren yaja Harun, shikuma Muftahu Galadima. “Waishin mikukeyi ne haka brother? Da girmanku da ajinku kuke danbe? danbe fa? Wannan wane irin kuma abin kunyane? Lallai da y'an jarida zasu samu labari gobe dasunci kasuwa sosai.....” Hankad'a Muftahu Galadima yayi baya, yay taga-taga zai fad'i, bai kuma kallon ko wanne a cikinsuba ya nuna Harun da d'an yatsa, “Mara kwakwalwa kawai, kafin ni ka kasheni ninan zan kasheka daga kai har munafikin ubanka, dak'ik'i kawai”. yana gama fad'ar haka yabar wajen zuwa cikin gida, taku yake kamar wani bajimi ya fito za6en sarauniyar k'yau. Daga Nuren har Muftahu da kallon mamaki suka bisa, shi kansa Harun maganar Galadima tasakashi girgiza, kardai guy d'innan yana sane da wanene ni tun tuni amma ya k'yaleni? da k'arfi ya fisge shima daga jikin Nuren yana kaima Muftahu duka, “Munafiki dakai zan fara”. Saurin kare kansa Muftahu yayi, Nuren yakuma yunk'urin rik'e Harun, danshifa abin yafara d'aure kansa, kowa yasan Harun aminin Galadima ne Na kusa, yau kuma miya had'osu haka? harda zancen kisa? Galadima yanada matuk'ar zuciya, idan ransa ya 6aci babu ubanda ke gane kansa.... Fad'a dai Neman komawa yay ga Muftahu, saida su Ameer sukazo suka rirrik'e Harun, cak suka d'aukesa yana fisge-fisge da fad'ama Muftahu magana suka shiga dashi ciki. Nuren ya kalli Muftahu dake murmushi yana gyaran kwalar rigarsa. “Amma mike faruwa kuma haka? Yau Sameer ne ke fad'a da Harun?”. Muftahu ya dafa kafad'ar Nuren, “'Dan uwa akwai abinda baka Sani bane, amma Na tabbatar yanzu zama sanshi”. Yana gama fad'ar haka yayi gaba abinsa, shima da kallon Nuren ya bisa, kenan shima yasan dalilin fad'an nasu ashe? jiki a sanyaye ya nufi wajen motar ya kashe sannan ya nufi gidan shima, a yanzu kam lamarin wanan case yafara rud'ar dashi, dan yanda Sameer keta abubuwa a tsakaninnan basuyi kama da nasa zarginba shi. Galadima Na kwance cikin kujera doguwa, tunda ya shigo anan yazufe, duk yanda zuciyarsa taso 6aci sai kalaman Munaya su danne su (mata kunga amfanin hikimar zance ga mazajenmu ko), zantuttukanta suka shiga dawo masa a rai daki-daki, tabbas a yanzu ba fushinsa bane abin buk'ata, jarumtar hak'uri ce, kamar yanda ta fad'a idan kwallo ta 6ata ba daina wasa akeyiba, wata kwallon ake d'auka ayi da ita, cikin lumshe ido ya ciji lips nashi yana wani miskilin murmushi. Daga Muftahu har Nuren dai ido suka zuba masa, ga Harun da aka saka a wani d'aki aka kulle sai bugun k'ofa yake yana fad'ar magana masu zafi akan Galadima. Mik'ewa Galadima yayi yana gyara rigarsa, ya kalli su Muftahu yana cire safar hannunsa, “bara naje gida”. Abinda kawai ya fad'a kenan yay ficewarsa. Tamkar sokaye haka suka bishi da kallo, yana fitowa ya iske sarkin mota a waje yana jiransa (Ashe dama ya biyo bayansu) da hanzari ya bud'e masa motar ya shiga, Galadima ya zauna yana sauke ajiyar zuciya a cikin kujera. Har suka Isa masarauta babu Wanda ya iya tankawa. Sarkin mota nayin parking baima jira an bud'e masaba ya bud'e da kansa ya fice, hadimai masu tsaron sashen Na masa barka da zuwa amma ko kallo basu isheshiba. Kai tsaye sashen Munaya ya nufa, babuko sallama balle Neman iso ya danna kai cikin d'akin. Laraba da samba da yara duk sunyi barci, Munaya kam takasa hakan, sai safa da marwa takeyi tun d'azun, taje d'akin Galadima yafi sau 7 amma bai dawoba, hankalinta a tashe yake da tunanin ina yaje a darennan? shida idon mak'iya kullum a kansa yake, dama kad'an suke nema ta cuta masa?..... Cak tunaninta ya tsaya lokacin da taji anyi sama da ita, zata fasa ihu yace, “yima mutane shiru”. A hankali yayi maganar, Dan haka ta had'iye ihunta cikin sauri da mamakin abinda yayi, yana fitowa falonta ya ajiyeta yaja hannunta zuwa sashensa. Babu abinda zuciyarta takeyi sai dukan 50-50, miye yashiga kansa haka wai?. Basu tsaya a falo ba sai bedroom d'insa, dama tun a hanya ya fara cire jacket d'insa, suna shigowa yana ida cirewar, yay wurgi da ita a tsakar d'akin yakuma d'aukar Munaya suka fad'a saman gado. Tsoronsa yakuma shigarta lokacin dataji ya sakata jikinsa ya matseta, kaikace zai maidata a cikine. Cikin matse baki da sakin k'aramar k'ara tace, “wai minene haka yalla6ai?”. “shiiii!!”. Yafad'a yana d'ora yatsansa d'aya akan bakinta, batada za6in daya wuce tayi shirun, sai zuciyarsa dake wani irin bugu da k'arfi, hannunta ta saka a saitin zuciyar tana karanto addu'a. Duk abinda takeyi yana jinta, hawaye masu zafi suna kwarara masa a ido, saidai tacan gefene shiyyasa Munaya bata saniba, tsawon lokaci muna a haka, har zuciyarsa tafara dai-daita bugawa, takoma normal, sai ajiyar zuciya da k'ok'arin dai-daitar numfashi kawai yakeyi, a haka barci ya kwasheshi, saida nabari barcin yayi nisa sannan nazare jikinna cikin dabara da k'yar nabarshi, Dan Dana motsa saiya k'ara k'ank'ameni, da k'yar dai Na kwaci kaina Na maye masa gurbina da filo, cikeda tausayawa nake kallonsa ina hawaye, a haka Na cire masa takalman k'afarsa, naja bargo Na lullu6a masa, addu'ar barci nayi Na tofa masa, gudun karna ta6ashi ya farka na tofa d'in, Na kashe wutar d'akin nabar da barci kawai na fice ina share sauran kwalla. 'Dakin da Sauban yake kwance na kwankwasa, yataso cikin mayen barci ya bud'e, ganina yasashi watstsakewa babu shiri, “Aunty gimbiya lafiya kuwa?”. “lafiya lau Yaa Sauban, cazan dama kaje d'akin Abban su Amaturrahman ka kwanta tare dashi, naga kamar bayajin dad'i, ba'asan mi dare zaiyiba”. Kansa ya jinjina yace, “to aunty”. Tunda na koma d'aki sai damuwa ta katantaneni, na dad'e ban barciba, daga k'arshema saida na saka karatun Qur'an da k'ara kad'an sannan barci ya saceni batare da na shiryaba. *_Washe gari_* Tunda asuba kasa hak'uri nayi na nufi d'akinsa. Mamaki da kunya suka kamani, Dan ganinsa ragal ya fito wanka, gashi d'aure yake da towel, Sauban yafita saishi kad'ai. Da sauri na juya da nufin komawa amma sai naji an rik'o hannuna, kasa juyawa nayi, yamatso dani ya saka a jikinsa, laimar ruwan da k'amshin sabulun sai suka sakani lumshe ido, ya d'ora hannunsa d'aya bisa cikina ya rik'e hannuna da d'aya, kansa a dokin wuyana yace, “Thanks matar Contract”. Kamar bazanyi magana ba sai dai nayi, Dan karna barta ta kasheni, nace, “Tausayinsu Abie ya sakani, kaji mijin Contract”. Murmushi yayi mai sauti yana shinshinar dokin wuyana, hannu na saka na ture kansa ina fad'in “ka dinga kula fa”. Ya kuma maida hancinsa a wajen, cikin tura hannunsa a rigata yace, “Nida sadakina gwaggo tsiwa”. Ban tanka masaba na fisge jikina, shima saiya barni yana wani bina da ido cikin k'ank'ancesu da miskilin murmushi. Saida naje bakin k'ofa na tsinkayi muryarsa yana fad'in “Kinzo kawai kin karyamin alwala”. Babu shiri na juya Na kallesa, amma saiya basar tamkar bashine yayi maganarba, yama juya ya nufi hanyar bathroom. Kwafa nayi na ida ficewa. Bayan Galadima yakuma d'auro alwala ya fito saiya iske tea a mug da da cake a k'aramin bowl, ya d'anyi luuu da ido tamkar zai lumshe saikuma ya bud'e yana murmushi da shafar kansa. jallabiya ya saka yay salla a d'aki, bayan ya idar yazauna yasha tea d'in, dama jiya baici komaiba ya fita, yunwa yakeji, koda ya kammala saiya fice abinsa. Sashen mai martaba ya nufa hadimai nata zubewa suna kwasar gaisuwa, sukan samu amsa iya kan la66a da d'aga hannu, da haka harya Isa. Saida jakadiya tamasa iso sannan ya shiga, a k'aramin falon mai martaba dayake hutawa idan baya buk'atar ganin kowa har matarsa ya iskeshi, yayi mamaki kwarai, dan inhar mai martaba ya shiga falonnan kofa mama Fulani sai dai tayi hak'uri da ganinsa. Yana kishingid'e saman tattausar darduma da aka k'awata da kilisa ta asalin sarakuna masuji da tsantsar mulki, ga tumtum da sauran kayan k'awa, an saka na'urar dake d'umama d'aki kad'an saboda yanayin sanyin safiya musamman na wannan lokacin da bazara take kunno kai. Da hannu mai martaba yayma Galadima nuni da kusa dashi, Galadima yaje ya zauna yana tankwashe kafafu, cikin girmamawa ya risinar da kai yana fad'in “barka da asuba Abba”. Mai martaba ya jinjina kai yana lumshe ido da amsa cikin fad'in, “barka dai yarona, ina d'iya ta da abokaina da amarya?”. Murmushi Galadima yayi, kansa a k'asa yace, “duk suna lafiya Abba”. “Masha ALLAH, yaya jikin naka to?”. “Na warke ai Ranka ya dad'e”. “To Alhmdllh, haka akeso ai, Yaya maganar tafiyar ita mai d'akin naka? duk da dai abin yazo da tsoratarwa yakamata a ayi yanda kowa yakeyi Sameer, ALLAH shine mai tsarewa, kuma zai tsaresu, domin ransu a hannunsa yake, idan an hanata zuwa an tauye hak'inta, zakuma ta iya ganin hakan kamar ita danba wata baceba, nagama shirya komai yau za'amata rakkiya kamar yadda akema kowacce mace dake aure a masarautarnan”. Cikin had'iye yawu da wani Abu daya tokare mak'oahinsa yace, “to Abba, ALLAH yasa hakan shine mafi alkairi, nima zuwa yamma zan koma India, akwai abubuwan da zanyi na kwanaki biyu zuwa uku zan dawo”. Mai martaba yay murmushinsu irin na manya, cikin jinjina kai ya ajiye k'aramin mug d'in hannunsa mai k'yau yana fad'in “ALLAH ya taimaka, Maybe kana dawowa nima zanje insha ALLAH”. Galadima yace, “ALLAH ya kaimu”. Daga nan sund'an cigaba da ta6a hira, a haka jakadiya ta shigo nemawa matawalle iso, yabada izinin a shigo dashi. bayan shigowarsa da yin gaisuwa sai suka d'ora hirar su uku gwanin sha'awa da birgewa. da Wanbai yazo gaida Sarki jakadiya ta sanar masa ai Galadima da matawalle suna ciki, shi komawa yay wai yafasa gaisuwar, jakadiya ta ta6e baki tana 6azgar goro da fad'in “kaikuma kasani gwandararren banza, kai koma y'ar k'autarnan ta jinin girma ba iyawa kaiba, dakasha kanu da sirrika a wajena wlhy”. duk a hankali take maganar yanda kowa bazai jitaba🤣. Saida gari yay tangaran da haske sannan Galadima da matawalle suka fito, suka bar Sarki zaiyi shirin zuwa fada. Koda Galadima ya dawo sashensa wajensu Munaya ya nufa, saboda jiyo kukan yaransa. Ya iske Ashe wanka ake musu, Munaya kuma tana wankan itama, sai Samha da Sauban keta faman jijjigarsu a kafad'a, Abdurrahman kuma yana hannun laraba tana masa wanka. duk gaidashi suka shigayi, ya amsa musu cikin jinjina kai da lumshe ido, baki kam ko motsi bai yiba. Samha ta kawo masa Amaturrahman dake hannunta, bai d'auketa ba, ya dai shafa kumatun yarinyar yana murmushi, sai tayi shiru tana kallonsa kaikace tasan wanene. Murmushinsa ya fad'ad'a yana jan d'an hancinta. Samha tace, “Uncle Sam ALLAH Amaturrahman tafi su Abdurraheem wayo, shiyyasa nafi ji da ita”. Murmushi yakumayi, ya shafi muskar Samha itama tareda d'an bubbugawa, hakan ya sakata fahimtar yau babu y'an maganar a kusa. Saima ya juya yay ficewarsa abinsa daga d'akin. d'akinsa ya koma ya sake wanka da shirin fita cikin wani d'anyen boyal fari tas, anmasa surfani da golden color sai walk'iya yake da d'aukar idanu, takalmansa na ainahin masu sarauta half cover da lankwasarsu a gaba suma fari da kwalliyar Golden d'in, ya matsa gaban Mirror yana kallon kansa da d'aura a gogo, ganin komai dai-dai ya d'auki turarensa ya fesa kala-kala sannan ya zuba wayoyinsa a aljihu da d'aukar links d'in hannun rigar yafice yana k'ok'arin sakawa. Da Sauban sukaci karo, yabisa da kallon birgewa, kai manyan kaya na matuk'ar k'awata k'yawun dirin yayansa, kuma sai akayi sa'a yana masifar sonsu, Dan ko'a India yakan sakasu fiyeda k'ananum kaya ko suit. Zungurinsa galadima yayi yana fad'in “baka sanni bane?”. Ajiyar zuciya Sauban ya sauke, yana sosa k'eya, “Yaa Sam please one pic.. Mana”. Galadima ya hararesa zai cigaba da tafiya, da sauri Sauban yakuma had'e hannanyen sa alamar rok'o. Galadima yay guntun tsaki, “kaiwai shin mikake da hotone? kullum baka gajiya da tarasu”. ya k'are maganar yana d'an dafe goshi. Shidai Sauban ya marairaice, babu yanda Galadima ya iya dole ya yarda yamasa hoton, harda zuwa sukayi tare. Shidai Galadima ya girgiza kai kawai ya nufi sashen Munaya. Ya isketa taci gayunta cikin doguwar riga ta popul d'in material, tayi d'as da ita, bazaka ta6a kallonta kace itace da yara uku ba, tana zaune tana bama Abdurraheem nono, sauran kuma suna hannun Samha, laraba tafita.. Zama yay kusada Munaya ya kar6i sauran yaran a hannun Samha, ya d'an rankwafa kan Munaya yana kama hannun Abduraheem data cire a nono ta gyara rigarta, da sauri ta d'ago tana kallonsa da mamakin koya manta Samha na d'akin dazai wani shige mata, shima kallonta yayi yana d'age gira d'aya fuska babu walwala. Hakan kam saiya bama Samha damar yimusu hoto jiki na rawa, Dan ba k'aramin bada kala sukayiba😘. Hasken camera d'in ya saka su d'agowa duk suka kalleta, wani ta sake k'yastawa ta fita da gudu. Munaya ta saka hannu tana toshe bakinta saboda dariyar dake Neman kufce mata, shikam kwafa yay yana fad'in “zan kamaki ne Dan k'aniyarki, yara duk sunbi sun rainani”. Dariyar Munaya ta fito Dan takasa rik'eta, hararta yayi dukda dariyar tata tamasa k'yau, yad'an rankwasheta akai, “kece kika sakasu ko? dama ai Sauban shima titsiyeni yayi”. Daina dariyar tayi ta turo baki gaba tana tsafa inda ya rankwasheta, “yoni mizanyi da wani hotonka malam”. “waya Sani ko sokike ki mallakeni”. Baya Munaya tayi tana kallonsa, ya wani basar tamkar bashine yay maganarba, ya hauma yaransa wasa dukda basusan mima yakeyiba. Dan gwarar da Abdurraheem tayi gefensa tana mik'ewa, “Humm, ko inason mallaka bazan mallaki abinda bai minba”. Yi yay tamkar bai jita ba, yabama yaransa gaba d'aya hankalinsa. Munaya taji haushin k'in kulatan da yayi, yakai mintuna 30 a d'akin kafin yay kissing kumatunsu ya ajiyesu. inda Munaya take tsaye jikin mirror tana kallonsu ya nufa ta d'auke kanta tana maidawa gefe. Gabanta ya tsaya daf har tanajin hucin numfashinsa, hannunsa duka cikin aljihun rigar boyal d'insa 3Quarter, “Na dawo gareki, idan kin Isa maimaita abinda kika fad'a”. Tasan halinsa da makomar maimaicin, shiyyasa ta ta6e baki tana cewa, “aini ba'a sakani abinda ban niyaba”. Bakinsa ya ta6e yana murmushin gefen baki, “matsoraciya kawai”. yafad'a yana juyawa zai fita, saida yaje bakin k'ofa sannan ya kalli agogonsa, “kuzama a shiri, dana dawo....”. Bai k'arasa ba yay ficewarsa. Da mamaki Munaya tace “daka dawo? To daka dawo za'yi mi?”. Batada mai bata amsa dan haka ta share ta koma kusada yaran. Da hanzari Su sarkin Mota suka mik'e, aka bud'e masa mota ya shiga, sashen da aunty Mimi take suka fara zuwa, ya shiga Dan yasan tana nan tanajin haushinsa akan fitar jiya. Aiko a falo ya isketa zaune a dining tana breakfast, hadimanta nata kaikawon gyara 6angaren, dining d'in ya nufa yaja kujera ya zauna, idonsa a kanta, ta shareshi tamkar batasan dashiba, shima baice uffanba ya d'auki spoon ya saka a plate d'in da take cin Arish, harararsa tayi, shima ya rama yana ta6e baki da basarwa ya cigaba da cin Arish d'in hankali kwance. Kallonsa ta tsaya yi kawai da mamaki, takai hannu ta daki damtsen hannunsa, shafa wajen yayi yana bud'e baki, saikuma ya kwa6e fuska alamar shagwa6a. Dariya Aunty Mimi tayi tana sake dukansa da fad'in “kadai girma rigimamme”. Yay Murmushi tareda kwantar da kansa gefen kafad'arta, a hankali yace, “kin daina fushin dani to? kinsanfa babbar ya uwa”. Murmushi tayi itama, ta shafa kansa tana fad'in “bazan iya fushi da kaiba ai my k'ani”. Yace, “Nagode Auntyna”. yafad'a yana tashi zaune sosai. Mug d'in tea d'in hannun ta ta mik'a masa, ya girgiza kansa. Tace, “miyasa?”. Iska yad'an furzo daga bakinsa, yace, “K'anwarki tamin d'ura tunda asuba Dan mugunta”. Aunty Mimi tayi dariya, “'Dan rainin wayo, inama laifin daka samu mai maka d'urar, kama tunamin, Yaya maganar tafiyarta gida?”. Saida ya rage fara'a sannan yace, “mungama magana da mai martaba” ya kalli agogonsa da cigaba da fad'in “yanzu zand'anje wani waje, insha ALLAH zuwa 2 to 3 zan dawo, basai yamma bane?”. “To Alhmdllh, naji dad'i da mai martaba yasa baki, dan da wannan taurin kan naka bazaisa ka saurari kowaba”. Mik'ewa yay yana ta6e baki, tareda cewa nayi nan, saina dawo, kudai zama cikin shiri jirgin 7:30pm zamubi”. “ALLAH ya tsare ya bada sa'a”. “Amin” ya amsa yana ficewa. Aunty Mimi tayi murmushi da binsa da kallo, tana tausayin k'aninta da gwagwarmayar rayuwa ta zauna jiransa tunkan yazo duniya, ALLAH dai ya kawo iyakar komai dan shima yasamu kwanciyar hankali. Nace, “amin aunty Mimi mu😘👍🏻”. ******************* Koda Galadima ta fita waya ya kira, Wanda suke wayar ya tabbatar masa k'arfe 11:00 dai-dai Alhaji Shehu Darma zaibar gidansa. Galadima yay murmushi, sannan ya kalli sarkin mota. “Baseer!” Sarkin mota ya amsa da “na'am Ranka ya dad'e”. Kwantar da kansa yay jikin seat d'in yana cewa “Zamu banbanta tafiya dasu, dan haka a plaza zamu kar6i mota hannun Saleem, da ita zamu samu Shehu, itace irin motar dazai shiga”. Cikin mamaki Sarkin mota yace, “Amma ranka ya dad'e ta Yaya? Kasanfa yanada bodyguards kuma masu had'ari”. Murmushi Galadima yay yana d'agowa, yace, “Duk had'arinsu Muhammad Sameer Saifudden yafisu, kaidai yi abinda nace”. Da to kawai sarkin mota ya amsa cikeda girmamawa................✍🏻 😨🙆🏽Galadima ma yazama kidnapper, readers saiku kiyaye⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀🤣. _Masu nemo picture's d'in mutane suna cewa wane da wane canta matse muku, nidai banyi cover d'in RAINA KAMA ba, sannan ban fad'i kamannin mutum ko guda d'aya a buk d'inaba balle mutum yace na siffanta da Wanda kuke yawo dashi, naga wasu suna fad'ar duk maganar datazo bakinsu akan hoton babu taunawa, Ku kama kanku bansan rainin hankalinnan, yafara isata hakanan kuma, bazai yuwu kulum ina asarar data da lokacina ba sannan kuzauna kuna yankama mutane magana batare da kun duba cancantar fitarta ba, please ya Isa haka, ya isa Wanda bazai iyaba babu lali babu tilas, idan kungama wannan kunga batakai mukuba saikuma Ku tsokalo wannan, shin wane irin rayuwane hakan dan girman ALLAH🤦🏻‍♀, salon cikin Luke d'auka ko k'alk'yalin duniya?, bazaku ta6a magana akan Abu mai muhimmanci da amfaniba sai Mara amfani._ *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~BOOK 3~ 👉🏻3⃣ & 4⃣ ................Suna Isa plaza Saleem ya fito, dan yana ganinsu ne ta CCTV, Galadima yay k'asa da glass 6angaren da yake, idonsa akan Saleem dake fitowa, ya k'araso yana rissinawa da gaisheshi, hannu kawai ya d'aga masa, Saleem ya mik'a masa key d'in motar yana fad'in “gashi ranka ya dad'e”. Kansa ya girgiza masa, sannan ya bud'e baki yana fad'in “ai Kaine da kanka zakaja motar, mu zamu bika a bayane”. Da “to” Saleem ya amsa, ya juya ga motar ya shiga. Haka suka tafi su Galadima a gaba Saleem nabin bayansu, suna tafiya Galadima nayin waya har suka isa inda aikai musu kwatance, wajen wata ma'aikatane, motocine birjik a wajen, alamun sunada yawa a ciki, daga d'an nesa suka tsaya, kusan mintuna biyar saiga wani dattijo ya fito tsakanin motocin jikinsa na rawa, harya k'araso wajen motar su Galadima idonsa akansa yake, ta window ya lek'o, amma sai Galadima yay masa nuni daya zagaya ya shigo. Ya zauna a d'arare yana gaishe da Galadima, cikin y'ar sakin fuska Galadima ya gyara zama yana kallonsa, “Baba Rabilu ka kwantar da hankalin, insha ALLAH zaka ku6ta kuma zaka samu y'ancinka, ni namaka wannan alk'awarin, bazaka ta6a taimakona nabari ka wulak'anta ba insha ALLAH, a hankali iyalanka da duk wani dake tare dakai zai fahimci baka mutuba, yanzu mi sukeyi cikin nan d'in?”. Baba Rabilu ya had'iye yawu, muryarsa na rawa yace, “Ranka ya dad'e ban saniba wlhy, amma abinda na fahimta shine lallai sunfara farga dakai, dan naji jiya mai wani a cikinsu yana waya wai kaima lokaci yayi dazasu maka irinna mahaifinka, dan kana neman zamewa rayuwarsu barazana”. Murmushi Galadima yayi, yana cije lips, “karka damu baba Rabilu, wannan ai a hannun Ubangiji yake, yanzu dai ga mota nan ankawo, saika kar6a, zakayi gaba, mukuma zamu bika a baya da y'ar tazara, inason kafinma su d'auki hanya komai zai wakana, su Ameer a shirye suke suma”. “shikenan ranka ya dad'e, ALLAH dai yabamu nasara, kaikuma yabaka kwarin gwiwa da k'arfin zuciyar abinda ka faro, ka ruguza rundunar wad'annan azzaluman da kullum cikin zaluntar bayin ALLAH suke ba a saniba, wasu kuma sunsani tsoronsune ya hanasu magana ko d'aga murya.....”. ya k'are maganar cikin sharar hawaye’. Shiru kawai Galadima yayi yana kallonsa, shima zuciyarsa sai suya da k'una takeyi, saidai yanata ambatar sunan ALLAH kodan neman sassaunci, ajiyar zuciya ya sauke da furzar da huci, yace “shikenan muje ko, dan zamu iya rasa damarmu”. Jin jina kai Baba Rabilu Yayi, ya fita yana rufo k'ofar, hawayen da suka cikama Galadima idone ya sakashi d'aukar glasses d'insa ya saka yana had'iye abinda ya toshe mak'oshinsa, yagaji hakanan, buk'atarsa yanzu kawai k'arshen al'amarinnan yazo kowa ya huta, shima ya gina rayuwarsa data y'ay'ansa cikin salama. Sun isa k'ofar gidan Alhaji Shehu Darma, amma baba Rabilu ya tsayane nesa da gidan, sai motar su Galadima Ce ta k'arasa har gate. Mai gadi yasan Galadima, dukda bawani zuwa gidan yakeba sosai, dan haka babu wani bincik'e-bincike ya barsa ya shiga. Gidane babba na alfarma, Wanda kallo d'aya zaka masa kasan lallai an kashe dukiya ta musamman. Galadima yana zaune a mota bai fitoba, sarkin mota ya fita domin nema masa iso, mintuna dabasu wuce 3 ba saiga P.A d'in Alhaji Darma tare da Sarkin mota, shine ya bud'e ma Galadima mota ya fito yana mai masa barka da zuwa. Yay masa iso har cikin gida falon Alhaji Darma na saukar bak'i masu muhimmanci. Zamansa babu jimawa aka cika masa gaba da kayan ciye-ciye, kai kace jiranshi suke, motsi Galadima bai yiba balle ya nuna alamar zaici, saima latsa wayarsa kawai yakeyi hankalinsa kwance, ga iskar AC na ratsa ga66ansa, kamar daga sama yaji ance “laaah Kaine a gidanmu yau?”. Da farko sharewa yay yak'i koda motsawa, mikuma ya tuna saiya d'ago a nutse ya zuba k'yawawan idonsa a kanta, gabansa yad'an fad'i, wannan ai yarinyar da suka ta6a had'uwane a jirgi, sannan itace suka kuma had'uwa a airport har yayma Munaya Abu dantaji haushi, to mitakeyi ana........? Tunaninsa ya kuma katsewa lokacin da ta tafa hannayenta guda biyu a saitin fuskarsa, firgigit ya dawo hayyacinsa, amma saiya basar kawai ya maida kansa ga wayarsa yana cigaba da danne-danne. Tana niyyar yin magana saiga Alhaji Shehu ya shigo, Galadima yakuma saita camera d'in wayarsa danya ga yanayin da Alhaji Darma zai shiga idan ya gansu. Ilai kuwa da mamaki ya kalli yarinyar, ya bud'e baki kamar zaiyi masifa saikuma ya had'iye yana fad'in “kekuma waya kawoki nan Rumaisa?”. Dariya tayi cikin nuna ita ta6ararriyace zata fara zaro zance ya harareta, sannan ya nuna mata k'ofa da hannu, “wannan ai iskancine, ya za'ayi daga yin bak'o kiwanizo ki tsaya masa akai, kedai uwarki tagama lalataki, ta6ararki tayi yawa w.......” Katseshi Galadima yay da fad'in Afuwa Alhaji, maybe itama uzurintane ya kawota”. “Shikenan Sameer, amma abunne babu dad'i ai”. “babu komai”. Galadima ya fad'a cikin lumshe ido. Gaisuwa sukayi da tambayar juna Ahali, Alhaji Darma yace, “ina Haneefa? had'uwa tayi wahala, siyasa ta 6oyemu, tunda kunk'i bani dai”. Murmushi kawai Galadima yay baice komaiba. Alhaji Darma daduk yakasa nutsuwa da wannan zuwa na Galadima ya mik'e yana fad'in “kad'anci wani Abu Sameer, ina zuwa dan ALLAH”. Galadima ya jinjina kai kawai, Alhaji Darma na fita ya murmusa, bodyguards biyu da suka shigo tare dashi d'aya ya fita, d'ayan harzai fice saiya dawo baya kad'an, wani Abu ya ajiyema Galadima ya fice shima da sauri. d'auka Galadima yay ya saka a aljihu, sannan yamik'e alamun shirin tafiya, hakan ya nuna dama can abinda yazo nema kenan. A tsaye Alhaji Darma ya iskeshi, cikin mamaki yace, “Sameer yana ganka a tsayene?”. Cikin murmushin dole Galadima yace babu komai Alhaji, zan wucene, dama hanyace ta biyo damu, shine nace bara na shigo mu gaisa an dad'e ba'a had'uba”. “Aiko ka k'yauta, ALLAH dai ya saka da alkairi, ai kafi Haneefa da saitazo k'asar sau nawa bata tuna damuba”. Nanma dai murmusawa Galadima yayi kawai. Har harabar gidan Alhaji Darma ya rako Galadima, saida yaga ya shiga mota sannan hankalinsa ya kwanta, ya sauke ajiyar zuciya yana goge zufar fuskarsa data wuya. Sarkin mota yay murmushi, “Ranka ya dad'e yanzu kam komai ya kammala, d'an shegiyarnan shima yazo hannu”. Galadima baice komaiba sai ciza lips kawai da yayi. Guri suka kuma samu suka tsaya, duk motsin shiga da fitar gidan akan idon sune, suna nan zaune har Motocin Darma suka fito, suna fara tafiya baba Rabilu ya take musu baya, su Galadima kuma suka fara binsu nesa-nesa, can tafiya tad'an fara Nisan daba mai yawaba wani go slow Mara dalili ya tsayar dasu, Ameer daya zama mai bada hannu a yau a hanya data rabu biyu cikin hikima ya nuna motar da Alhaji Darma yake ciki yana sanarma driver d'in ya fito ya duba tayarsa. driver dake shirin fad'ama Ameer bak'ar magana Alhaji Darma yamasa tsawa akan ya fita ya duba mana, jikinsa na rawa ya fita, shikuma Alhaji Darma ya maida kansa ga duba newspaper d'in hannunsa. Da Sauri Baba Rabilu ya fito daga motar da yake ya maye gurbin driver Alhaji Darma, akuma time d'in Ameer yabasu hanya, shikuma wancan Driver yana can sagare da baki wai yana duba tayar mota, ganin motar tayi gaba sai yashiga k'ok'arin binta, Ameer ya dakatar dashi da fad'in anfa matsarne saboda ta tare hanya, bagasu a wannan hannunba inda zakaji dad'in dubawa”. Tsaki driver yayi yanama Ameer kallon banza, ya matsa ga Motar dake a fake ya shiga yana k'ananun magana, “wlhy Alhaji yaronnan k'arya yakeyi, irin y'an iskan yarannan nema fa masu shan kwayarsu suyi mankas suzo sunama mutane dabanci a titi, yakamata ad'au mataki akan irinsu”. Shiru dai yaji Alhaji bai amsaba. daga nan shima sai yayi shiru, duk zatonsa ko Alhaji baya buk'atar magana ne. A can kuwa tuni baba Rabilu yayi ciki da Alhaji Darma, dan harya d'auki hanya Su Galadima na binsa a baya, Alhaji dai baisan wainar da ake toyawa ba, hankalinsa nakan jarida🤣😜. Su kuma can sun d'anyi nisa da tafiya Driver dai yaga yanata surutu Alhaji ko tari bai yiba, saiya waigo yana kallon bayan, babu shiri ya taka birki da masifar k'arfi, jikake k'uuuuuu!!!! Gabbbb! Ya bigi motar gabansa, mota saita fara katantanwa a titi, nanfa mutane suka tsaya kallon abin al'ajabi, sauran motocin Alhaji Darma ma duk suka tsaya. Da k'yar dai wannan mota ta tsaya, jama'a suka zaro driver da k'yar, nan mutane na kaya-kaya akaisa asibiyi karya mutu tunda yana numfashi, sukuma bodyguards d'in Darma hange-hangen ina za'a ganoshi shima suke, saidai alama ta nuna motar mutum 1 nema a cikinta. Tofa babbar magana, an dai d'auki driver da gaggawa zuwa asibiti, yayinda bodyguards suka shiga jaje sukuma. Kafin kacemi gari yafara d'auka ta silar social media, saikuma y'an sanda. Jin mota ta tsaya Alhaji shehu ya d'aga kai danya tambayi ko lafiya? yasan dai ko quarter d'in inda suka nufa basuyiba, to miye na tsayawar?. Baki bud'e yace, kai Antoni miye haka? gidan uwarwa ka kawoni nan kuma?”. Baba Rabilu ya lek'o da kansa yana Murmushi, “Aboki aiba Antoni baneba”. A matuk'ar firgice Alhaji Darma ya jefar da jaridar hannunsa, jikinsa na rawa da taune harshe yace Alhaji Rabeelu? Dama baka mutuba?”. “Mutuwa ai sai kwana ya k'are abokina, ganidai yau kam harda tuk'aka”. Cikin matuk'ar tsawa yace, “Karya kake munafuki, wlhy ka mutu saidai idan fatalwa kayimin, dafa hannunsa na kasheka shekaru 19 kenan?. Toko fatalwarka Ce yanzu itama zan kuma kasheta”. ‘yay maganar yana waige-waigen neman makami, amma babu. Baba Rabilu ya bud'e motar ya fita yana dariya, bud'e ma Alhaji Darma k'ofar shima yana fad'in “maza fito ka kuma kashe fatalwata.....” Aiko a harzuk'e ya fito, saida kuma wata rikitarce takuma kamashi ganin Galadima tsaye a jikin motar dake kusada wadda yake, ya hard'e hannuwansa a k'irji yayi wata tsayuwa mai sunam firgita mak'iyi. baya Alhaji Darma yay taga-taga zai fad'i ya dai samu ya dafe mota jikinsa na tsuma, cikin rawar murya yake nuna Galadima da hannu yana fad'in “S...S..Sameer! ba yanzu muke tare dakaiba a gidana?”. Galadima yay wani murmushin gefen baki yana gyara tsayuwa, eyeglasses d'in idonsa ya cire sannan yasa handkerchief ya goge fuskarsa, glasses d'in da handkerchief ya maida cikin aljihu, cikin d'age gira yace, “Nine kuwa tabbas SD, dan yau kaiba mai wancan sunan dana Sani bane a gaba na........”. Katseshi Alhaji Darma yayi, “kai Sameer! Kardai ka yarda da zancen wannan fatalwar?, wlhy fa Fatalwane, shekararsa 19 da mutuwa, karka yarda da munafuncinsa, kafa tuna nid'in wanene a wajenku, ta ya za'ayi na iya cutar daku? Ka yarda dani domin ALLAH”. murmushi Galadima yakuma saki, ya taka a hankali zuwa gabansa, yatsansa d'aya ya saka yana shafar girarsa, yace “SD aishi mugu dama bashida kama, bakasan yanzu babu kasuwancin dayafi yad'uwa a duniyaba sama da cin amanar juna, kuma na jikinka ke maka. Waynot ka Adana kalamanka ko zasu maka amfani nan gaba k'ad'an”. Yay Salute nashi yana ra6ashi ya wuce zuwa cikin gidan. “Sameer! Sameer!! ka saurareni mana”. Alhaji Darma keta fad'a kamar zai had'iye harshensa. Ko sau d'aya Galadima bai juyoba yay ciki abinsa. Wannan damar Alhaji Darma yay amfani da ita wajen harin baba Rabilu, amma sai su Ameer suka zagayeshi, cikin mamaki ya kalli Ameer d'in, danya ganesa sarai. Ameer ya d'aga kafad'a yana ta6e baki alamar bashida matsala😂.................✍🏻 🤦🏻‍♀yau dai typing d'in rowa nayi muku, gaba d'aya banajin yin typing d'in, kuyi manage kawai⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻_* *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~BOOK 3~ 👉🏻5⃣ & 6⃣ ...............Galadima ya shigo murmushi d'auke a fuskarsa, dattijon dake zaune a falon ya d'ago ido yana kallonsa shima fuskarsa d'auke da murmushin, k'arawa Galadima yayi garesa, ya zauna kusa dashi yana fad'in “Baffina kanata jirana ko?”. Kafad'arsa dattijon ya dafa, yace “karka damu d'an baffinsa, nasan aiki mai muhimmanci ne ya tsaidaka. ya k'ok'ari?”. “Alhmdllh baffi, munata fama”. “ALLAH ya dafa mana, yanzu ina shi Darma?”. “Gashi a waje tareda ma'aikata, zamu jira zuwan Sir Isa ne, dan asan miya kamata, bazai yuwu mu had'ashi da su Harun ba”. “Uhm hakan shine dai-dai kam, amma yakamata suma bayanansu kagama tattarasu waje d'aya ka kawomin, kasan abubuwa zasu cud'e mana a tsakaninnan, dan fatana insha ALLAH wannan shine case Na k'arshe dazan fuskanta a rayuwar aikina, shekara 1 kacal ya ragemin cika talatin a matsayin lauya, insha ALLAH kuma zan cikasune bisa alk'awarin gurfanar da dukkan mai hannu akan mai martaba”. Murmushi Galadima yay, idonsa cike da kwalla, ya had'iye Abu mai d'aci yana fad'in “ALLAH ya cika maka wannan buri baffi, lallai ina alfahari dakai amatsayin uba, Kaine ka nunamin hanya alokacin da k'ofa ta rufe min, Kaine ka tsallakar dani a lokacin da gada ta karye ina tsaka da tafiya, ga kuma gagarumin hadad'i mai cike da tarnak'in iska ya taso, badan kaid'in ba da jajircewarka da yanzu ruwan daya zuba ya shafe da tarihina dana ahalina, da ace wani zai saurari labarina saiya d'auka labarin film ne ko novel, ni karan kaina nakanyi zaman yin tunanin anya akwai mai irin rayuwata a k'asarnan? Dan mafi yawa a tatsuniyoyi da hikayoyi akejinsa, saikuma abin mamaki ga nawa a zahiri, a yankin k'asar hausa, yanki mai tsananin ruk'on addini da Al'ada, yanki mai mutunta ahali da zuminci, inhar a shekaru 26 baya za'a iya samun masu irin ayyukan su tanderu lallai akwai abin tsoro kenan a k'arni nagaba da y'ay'anmu zasu mu'amulanta, Baffi da ace d'an Adam Na iya za6ama kansa rayuwa da banzo cikin ahalin jinin sarauta ba, amma Alhmdllh, ina godiya da Ubangiji daya halicceni yakuma San cancantar fitowa daga cikinsu.......”. kukane ya sark'e Galadima, Baffi ya mik'a masa handkerchief yana girgiza masa kai alamar kar yayi. Murmushin takaici Galadima yayi, sannan ya kar6a handkerchief d'in ya tsane k'ananun hawayensa. Baffi yace, “Muhammad Sameer akwai labarai da tarihin mutanen da yafi naka sark'ak'iya da hargitsi wlhy, sometimes abinda mukan gani a films ko hikayoyin marubuta akwaishi azahiri, saidai inhar bai faru akanka ba ko waninka saikaga tamkar k'anzon kuregene, kasan su mutane sunfi amfani da abinda suka gani da ido wato zahiri, ko suka San Wanda ya Sani wato tabbaci, a shekarun da nayi INA aiki nahad'u da cases da dama masu sark'ak'iya da ban tsoro, nakuma halarci kotuna da Dama domin ganin wasu cases d'in, idan ka samu wani case kai kanka saika ringa kokwanton anya kuwa wannan da gaske ya faru d'in? Amma daka tsananta bincikema saikaga abinda yafi Na farko mamaki, lallai a ranar gobe kiyama wasu zasu kasance cikin bayi masu tsananin kunyata agaban Ubangiji, Dan wata shari'a Ubangijine kawai mai iya mata, mu kammu acikin lauyoyi da alk'alai hummmm”. Baffi ya d'an bubbuga kafad'ar Galadima yana murmushi cikin takaici. Bai samu damar k'arasa magana ba akayi sallama, izinin shigowa ya bada, wani matashin dattijo da shekarunsa bazasu gaza 45 ba ya shigo, baikai girman baffi ba, sannan ya girmi Galadima sosai. Mik'ewa Galadima yayi yay salute nashi, dattijo ya murmusa yana kama hannun Galadima ya zaunar da fad'in “ni da kai adai bincika mai sarama wani”. Baffi yay dariya, “kudai kuka Sani da gardamarku wacce kullum bata k'arewa inhar kun had'u”. Bak'o mai amsa Sir Isa yace, “wai Yaya naga alhaji Rabilu zaune a waje suna sa'insa da banzan can?”. Nanma dai baffi ne Yakuma darawa, yace, “duk cikin aikine, dukkan wata magana dazai takalesa ya fad'a ai itama hujjace, kasanfa halin Alhaji Rabilu ai, shiyyasa nace masa da irin aikinku ya dace ba siyasa ba”. Sir Isa da yay dariya shima, yayinda Galadima ke murmushi, “Ai yalla6ai yanzu ma aikin dayake mana bashi da banbanci damu d'in, danya bamu damar sanin abinda tsawon shekaru muketa wahala da kaikawon sani”. “Wannan gaskiyane kam Isa, yanzu Yaya za'ayi da Darma kenan?”. Sir Isa ya gyara zamansa, yana saka d'an yatsa a baki alamar tunani, zuwa can yace, “inaga kam saidai mu nema wajen ajiyesa ko yalla6ai ya Adana mana shi, dan yakamata saimun kammala tattara komai a hannunmu bayan yalla6ai Galadiman mu ya dunk'ule kifaye a ragaya, idan sun mik'a wuya shima sai a sakashi a ayari ko?”. Baffi yace, “shawararka tayi kam, inaga yanzu abinda kasaba za'ayi, dan aiki da ilimi yafi aiki da agogo, kaike 6oyewa, kuma kaine akesa kanemo 6oyayye”. Murmushi Galadima ya sakeyi baice komaiba sai jinjina kai. Duk d'insu basu damuba, dan sunsan halinsa Na rashin son hayaniya tuni, ayanzuma suna d'an ganin canji fiye da shekarun baya, shiyyasa suka fara zargin ko (Hikimar matace take aiki?) Dan kad'an daga aikin mace ta tada gari, kuma kad'an daga aikin ta ta gyarashi. Sund'an tattauna har baba Rabilu shima ya shigo, wayar dayay recoding d'in dukkan musayar yawunsa da SD yabasu, babu Wanda baimasa jinjina ba, Galadima ya d'ora da musu godiyar hidimar da sukeyi a kansa tsawon lokaci. Suka amsa da cewar lallai mahaifinsa ya cancanci sumasa fiyema da hakan, dan yataka rawar gani shima a tasu rayuwar. Lokacin da suka fito abinda yabani mamaki shine su Ameer duk salute nasu sukayi suna k'amewa. Galadima basarwa yay, sai Sir Isa ne yay musu inkiyar su sauke hannayensu, baffi yay murmushi yana kallon Galadima dayak'i kallon kowa ta gefen ido. Sarkin mota dai yasha jinin jikinsa, musamman Basarwar da yaga Galadima yayi. SD dake zaune ya zuba tagumi yana kallonsu kawai ya janye hannunsa, cikin jinjina kai yace, “lallai duniya tana cike da abin tsoro, wai Isa kana nufin kaima wani abune a k'asarnan? Kai kuma babban munafuki Brr Usman Audu Tsanyawa! Ba kaine da kanka kaje kasamemu da albishir d'in ajiye aikiba? Ashe wannan k'aramin kwaron d'an cikinku kukema aiki?........” A tsawace Ameer ya katseshi, tareda d'aga hannu zai makeshi amma sai Galadima ya d'aga masa hannu. Sir Isa ne yay wata y'ar dariya yana matsawa ga Darma, yace, “Idan banda abunga Alhaji shehu kowama irin kune mai tsukakken tunani? Ai abin kallo bai k'are makaba saima nan gaba kad'an, kasan ita mota hanyarta kwaltace, birji ma idan tasamu bitake, balle dagwalon ruwa mai kayan datti, shikam jirgi miye gamisa da wannan? ko d'aga a tashi hanyar babu duk wad'annan, kaga kenan aikwai matuk'ar tazarar banbanci a tsakaninsu, kallon idoma tattancewa yake basai an shiga gasar tabbatarwa ba, kaikuma ai taka ta k'are, sauran shekaru sai a prison d'in dajin SAMBISA zaka idasu”. Dariya SD yayi, ya mik'e tsaye yana fad'in “iyaka dai Ku kaini police station, ina mai muku alwashin kwana d'aya bazanyiba a can, daga can a mik'amu Court, alk'alinma namune masu k'ananun basira, yanzu haka nasan sak'ona ya Isa ga y'an uwana, kafinma Ku kaini station d'in reshe ya juye da mujiya, dan dolene a kamaku da alhakin kamani kunga martabar wasu saita zube, mulkin da akema mutane homa da buri babushi kenan”. Murmushi Galadima yayi, dan yasan dashi yake, yad'an ta6e bakinsa yana cigaba da latsa waya hankalinsa kwance, Sir Isa da baffi da baba Rabilu, su Ameer duk kallon Galadima sukayi, don suji amsar dazai bada, amma saiya basar tamkarma baijiba. Saida ya kammala abinda yakeyi yay kiran Nuren suka kammala magana sannan ya kalli SD yana murmushi, “Wannan lissafin naka fa ya birgeni Alhaji shehu, saidai albishir d'in dazan maka nima shine, duk wani kira dazakayi ko ayi maka to zai shigo wayatane, yanzu haka driver d'inka yayi had'ari, rashin ganinka a motar kuma zantuka sun baje kowacce kafar yad'a labarai, Na tabbata dukkan labaran rana kaine shafin farko, hakama jaridun gobe masu fita, labarin nemanka da ta Yaya ka 6ata? Shine babban labari, sukuma abokan naka hakan zai tada hankalinsu, saisu fara zargin ko dai d'an tsohon Sarkine Galadima Sameer da wannan aiki?, dole kuma sufara bincike, bayan sun haukata y'an sanda wajen nemanka, daga haka kaga nikuma saina cigaba da samun hujjoji........🤦🏻 kai zaka samin ciwon kai wlhy”. Galadima ya karashe maganar da bud'e mota ya shige abinsa. Su Ameer duk suka shiga k'yark'yala dariya, saboda yanda Darma ya mugun shiga rud'ani da sakin baki yana bin Galadima da kallo harya shige mota. basu tsagaitaba saida Sir Isa ya tsaidasu ta hanyar d'aga musu hannu, yace, “Alahaji Shehu yadai? Kaji irin aikin masu basira ko? Kai! Kai! Harna tausaya muku lallai. Ameer! Kubi yalla6ai Galadima dashi, shikeda masaukinsa”. Angama ranka ya dad'e. Suka fad'a suna salute nashi. 🤦🏻‍♀lallai nimafa yau nashiga ciwonkan Galadima, shin wane laujene cikin nad'i kuma dabamu saniba haka? Nadai fahimci Su Ameer ba y'an iskan matasa bane, kamarma jami'an tsarone?🙆🏽. To Aunty Salama fa? Data kawosu a cakwakiyar. Masu karatu, kumuje zuwa dai, nasan komai yana gab da bayyana lallai kam.☹⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. __________________________ Galadima dai kam plaza suka koma, yayinda Nuren ya tari su Ameer a hanya suka bashi SD. Acikin Plaza Galadima yad'anyi zagaye-zagaye, saida ya tabbatar da komai dai-dai a wajen ma'aikatan sannan ya fito suka d'auki hanyar masarauta. ***************** Bayan fitar Galadima Aunty Mimi sashen su Munaya ta nufa, ta isketa har yanzu tana juya kalaman Galadima dabata fahimtaba. Bayan sun gaisa tabata Umarnin ta shirya dan za'a kaita sashen manyan gidan ta gaishesu da bangajiya sannan suga yara, inhar zaki tafi wanka bayan kwana d'aya da suna haka akeyi a masarautar, to amma su nasu Munaya yazo da Matsala, tunda gashi sai bayan kwanaki hud'u da suna zasu tafi, matan Sarkine kawai basa zuwa gida wanka. Kuyangi biyu sukaima Munaya shiri, itadai wannan lamari Na d'aure kanta, haka kawai da girmanka ace komai sai anmaka, dolene mai mulki yake kallon talaka ba komaiba, sauk'inta ma bakomaine Galadima ke bada fuskar ayi mataba, yama hana hadiman masarautar sakewa a sashensa gaba d'aya, sai iya wad'anda ya aminta dasu kawai. Yaukam tasha kallon kanta a mirror, hakan yakuma tabbatar mata da tuna mata agidanfa SARAUTA take, a kuma matsayin matar mutum mai girman rawani da matsayi a Masarautan. (Kusan dai mutuniyar taku da jan aji😉, ai saita kuma tsumewa tana basarwa🤣). Suma yaran an musu shirin dake nuna lallai Ubansu waninine a wannan masarauta, sannan suma ababen tattaline ga wannan kujera kwara 1 tal dakowa ke mutuwa da rayuwa a kanta a masarautar gagara badau☹. Sun sami rakkiyar kuyangi da Aunty Mimi, kowane sashe saida suka zagayashi amma a mota, an farane da fada. Yau itace ranar farko da Munaya ta shiga Fadar sarkin ta, yaukam taga abin mamaki, musalta yanda wannan fada ta k'awatu ai 6ata lokacine kawai, ammafa lallai komai yaji, ga Sarki hakimce bisa garagarsa cikin kwarjini irinna mutuntakar mulki, sarkinmu kenan kuma sirikinna ta wani fannini, daga ni sai aunty Mimi da kuyangi ukune muka shiga, kowanne d'auke da yaro d'aya a hannu. Fada cike take mak'il anata fadanci, Su Wanbai da talba duk ana ciki, hakimai da masu manyan muk'amai Na masarauta da wajen masarauta duk an hallara, kasancewar shine zaman farko Na wannan makon, kuma ana saka ran zuwan Governor ne da zaizoma mai martaba jajen abinda ya faru Na 6atan y'an uku, dan labarine daya zagaye kowacce kafa ta yad'a labarai da socia media Na k'asar nan, (kunsan dai abin manya duk k'ank'antarsa saiya fita, balle wannan da yazamo mai girma). Bayan Munaya da aunty Mimi sun zauna a k'asan lallausar darduma can gefe suka kwashi gaisuwa, dogarai suka amsa da yawun Sarki, sannan suka kuma gaisheda fadawa. Daga nanan aka amshi su Abdurrahman, y'an majalissar Sarki sukaita d'auka d'ai-d'ai suna saka musu albarka, da addu'ar fatan alkairi. Bayan fitowarsu sai sashin iyalan mai martaba, yau ma dai gimbiya zulfa bata fasa nunama Munaya da yaranta soyayyaba, daga Munaya har aunty Mimi basu San komaiba, dan haka sukaji dad'i da sakin jikinsu fiye da sauran matan sarki. Daga nanan sai sashen Mama Fulani, (kaga manya, Sarautar gagara badau a hannunku take, mama fulaninmu ta mutunci🤸🏻‍♀😂, ga irin naku manyan mata👍🏻) To kunsan dai mutuniyar taku, yauma dai cikin izzar mulkinta suka isketa, ita dama Aunty Mimi babu ruwanta, tana mata yanda takeso, shiyyasa babu y'ar habaici ko bak'ar magana tsakaninsu kamar Galadima, hakanne yasaka munaya samun tsira daga samun nata rabon, amma mama Fulani bata d'auki yaro ko d'aya ba, a hannun kuyangin ta gansu tana ta6e baki. Daga Munaya dai har aunty Mimi babu Wanda yay ko tari, to balle kuyangi dasuka zama takalmin takawarta, basu jimaba suka fito, haka sukaita zuwa sashe-sashe, basu sami Kansu ba saida suka Shiga ko ina . Sun dawo kusanda awanni biyu aka gama loda kayansu a mota Samha da Sauban suka shige gaba aka kai gidansu Munaya. Ita kuma sai zuwa yamma za'a mata rakiya. ************ Gidansu Munaya dai tunda kaya suka isa aka tsaya kallon-kallo, daga Sauban kam har Samha babu Wanda yamusu kallon arzik'i, yo sunaji da hayak'in girma dana mulki, innarsu Munaya da Munubiya da tuni tana gida kawai suka kula, harda sakin jiki dasu sukaita hira, sunmayi zamansu anan sai ankawo Munaya zasu koma. Nanfa matan gidan suka fara k'ananun magana, saidai babu mai yunk'urin d'aga murya saboda tsaro🤣. Oho innarsu Munu ma batasan sunayiba, balle Munubiya da yanzu saita ma gadama suke ganinta, ko yaushe tana d'akinsu, da anyi magana tace jego, dukda gasu Fiddausi a gidan duk suna wankan suma, Fauziyyace kan shigo susha hirarsu ta zuminci, amma sauran saidai idan an had'u a gaisa, kowa uwarsa Na kitsa masa munafurci a d'aki (🤦🏻‍♀gaskiya iyaye mata munada gyara babba ta wannan fannin, inhar zaka rayu gidan yawa sai kayi gamo da irin wad'annan matsalolin kuwa, ALLAH ya ganar damu baki d'aya dai). ****************** Su gadima Na shigowa masarauta ana kiran salla, hakanne ya sakasu yada zango a massalaci, saida aka idar sannan suka k'arasa sashensa, Duk agajiye yake, d'akinsa daret ya nufa, yashiga zame kayansa tun a falonsa, yana shiga ciki k'arasawa kawai yayi yashige bayi. Ya dad'e aciki kafin ya fito, baiko cire rigar wankanba yasha wani Magani ya kwanta, dan kansa ciwo yake masa. Cikin mintuna k'alilan barci yay gaba dashi. Munaya batasan ya dawoba, d'okin zuwa gida ya hanata barcin ranarma ita, sai yawan duba lokaci takeyi😂👍🏻. *_3:35pm_* Galadima ya tashi, saboda kiran wayarsa da akayi, idonsa a lumahe ya d'aga, a haka suka gaisa da Momma, ya tambayi Abie tace barci yakeyi, sunyi wayar kusan mintuna 15 haryaso makara fita sallar la'asar. Bayan yadawoma papi ya kira suka tattauna, sannan yakuma sabon shiri cikin Orange d'in yadi anmasa kwalliyar bak'i kad'an, yayi k'yau sosai, sai tashin k'amshi yakeyi, saidai fusakar kam babu alamun yasan miye dariya. A haka ya iso sashen Munaya, babu kowa daga ita sai yaranta da Khaleel dake barci a gefensu, itako wayama take latsawa, da alama game takeyi Kodai wani Abu. Sallamarsa ciki-ciki da k'amshin turarensa ya sakata d'ago ido suka kalli juna, yawani Basar yana shan k'amshi, hakanne yasaka Munaya sake kama kanta, ta gaisheshi, sau d'aya ya amsa ya zauna a bakin gadon yana shafa kan yaran d'ai-d'ai harda Khaleel. Handbag d'inta da mayafi dake ajiye alamar lokaci take jira kawai ya kalla, baki ya ta6e ya d'auke kai. Key d'in mota guda biyu ya fiddo a aljihu ya jefa min akan cinya. Ni harma Na tsorata na kalli keys d'in sannan Na d'ago na kallesa. d'auke Kansa yay daga inda nake, cike da k'asaitarnan tasa yace, bak'in kibama Abba, d'ayan kuma ki ajiye a wajenki, motar tana can, saboda ko wani abu yataso musamman kai yara asibiti sai wani ya kaiki cikin yayyenki, ki kulamin da yara, kuskure d'aya kikayi a kansu zand'au mataki mai tsaurine, duk abinda zuciyarki batayi na'am dashiba ki gaggauta kirana na sani, ki kula da Abdurraheem sosai, banda barinsa yana dogon kuka saboda doctor ya sanar mana yana d'auke da ciwon......”. Saikuma yay shiru yana furzar da iskar bakinsa. Masifar tsura masa ido nayi zuciyata Na bugu tamkar zata fad'o dan tsoro, sai tsuma nakeyi, babu shiri na taso na dawo inda yake, durk'ushewa nayi gabansa tamkar mai neman gafara, “Yalla6ai ciwon mi? Please ka k'arasa fad'an dan ALLAH”. lumshe idanunsa yayi yana cizar lips, “Ba abin tada hankali baneba ai, domin ALLAH daya d'ora mana yafimu sanin hikimar hakan, bagashi ni nakai lokacin da Magauta basuyi tunaniba”. Maganganunsa ya nuna minta cewar Abduraheem Na d'auke da Ciwon zuciya? kenan shima yayo gadon mahaifinsa?”. Matsowa nayi na fad'a jikinsa na sanya kuka, bashida za6i saina kar6ata shima ya rungumeni cikin yima Ubangiji tasbihin Neman dauriya da kar6ar jarabawa a duk yanda tazo. Bai hanani kukanba saida nayi mai isarta sannan na share hawayenna. d'agowa nayi daga jikinsa zan tashi amma saiya hanani hakan, cikin kunnenna yace, “Baki da kunya gaskiya, ban ta6a ganin uwa mara kawaici akan y'ay'an fariba saike”. Kunyace ta kamani, na 6oye kaina a jikinsa ina murmushi. Galadima ma murmushin yake yana shafa bayanta. Sun dad'e a haka sannan na tashi daga jikin nasa gudun kar khalel ya farka ya ganmu a haka, shima ya fahimceni, dan haka bai hanani ba. Yace, “Addu'arki yake buk'ata da taka tsantsan, dukda ba wayonmune zai hana Ubangiji ikonsa ba idan yaso, sai yakai watanni 6 zai fara ganin doctor insha ALLAH, ya mik'a mamin ATM d'insa, ga wannan dukdai abinda yataso saiki cira, amma a bimin kud'i a sannu ni talakane mai yawan buk'atu, ga Abdurraheem ya k'aru shima, to idan bawa bai nema kud'iba ai yagama shiga uku a wannan zamanin daba kowa ya damu da damuwarka ba, inadai kuma gargad'inki ki kula min da yara, yau zamu koma India, amma kwanaki uku zanyi insha ALLAH na dawo”. Nace, “ALLAH yabashi lafiya da dukkan al'ummar ANNABI, nagode sosai, saidai kuma inason kawai idan na tafi shi.......” Hannu ya d'aga min, “karki damu nasan maganar Aurenmu ne, kamar yanda na alk'awarin inhar komai ya fito kan shekara zamu rabu, inkuma ba a samu yanda akesoba shekara biyu inakan Sani, sauran bayani kibani lokaci zuwa kammala abinda ke gabana OK?”. ‘yay maganar yana kallonna’. Kaina kawai na d'aga masa ina had'iye abinda ya tokare mak'oshinna. Bai sake cewa komaiba ya mik'e yana kallon agogon hannunsa bak'i, “ku fito”. yafad'a yana ficewarsa. Da kallo kawai nabisa idonna yana cika da k'wallan dabasan na minene ba. ************** Munaya tasamu rakkiyar wasu daga masarautar, bisaga jagorancin Galadima da suke zaune a mota d'aya, daga ita har shi babu Wanda ya tankama wani koya kalli wani, shi tundama suka fito latse-latsen System yakeyi hankalinsa kwance, itama ta basar gefe tana kallon waje dukda glass d'in mai duhune. Sun Isa k'ofar gidan k'arfe 5:24pm, bayan su Aunty Mimi sun fita duk suka shige cikin gidan tareda Kuyangi. Munaya tayi yunk'urin fita amma sai taji motar a kulle, Sarkin Mota ta kalla sai taga harya fice, ta dawo da kallonta ga Galadima daketa aikinsa tamkar ya manta a mota yake. Shareshi nayi kamar nima bazanyi magana ba kamar yanda ya basar, amma saina kasa, na kuma kallonsa murya a sanyaye nace, “ka bud'emin mana, miye ma'anar zaman namu? Wanima saiya zargi wani Abu ai?”. Banza yay mani tamkar bazai tankaba, kusan mintuna biyu sannan yace, “idan sun zarga laifine? Naga Sadaki na biya”. “Hummm”. Munaya ta fad'a kawai tana d'auke kai. Saida ya gama shan k'amshinsa sannan ya ajiye lap-top d'in gaban motar yana matsoni. da mamaki na kallesa, “yalla6ai lafiya?”. “ita ta kawo haka”. ‘yafad'a yana wani ciccijewa da jawoni jikinsa’. Tamkar zan tsala kuka haka naji, dan naji zafi, mukaima juna kallon ido cikin ido, idona da kwalla tafara taruwa sai wani marmar yakeyi, matso da fuskarta yay sosai, cikin magana rad'a yace, “kin fara kewata ne?”. Baya naja da kaina ina tura baki da yamutse fuska, amma sai hannunsa daya sa ya tokareni ya dakatar dani daga matsawar, yakuma matsowa gaf, numfashin junanslmu na sauka a fusakar juna, a hankali yafara hura min iskar bakinsa saman ido, babu shiri na lumshesu, hawayen da suka taru suka zubo, sai kawai ya shiga sumbata ta. Tuni nabashi had'inkai babu wani gardama, saida yay yanda yakeso da ni sannan kowa yakoma gefe, wata y'ar k'aramar souvenir bag ya d'ora mani a cinya, sannan ya cire luck d'in motar, saida naja wasu Seconds nasamu dai-daita sannan ta bud'e na fice rik'eda bag d'in daya bani, ban yarda nasake koda kallonsa ba. Shima harta fice bai kuma kallon nata ba. Jiki a sanyaye nashiga gidan, matan gidanmu duk suna falon innarmu gaida bak'i, ina shiga muka rungume juna nida Munubiya muna hawayen da ita Munubiya tana tayani ne, nikuma bansan dalilin yinsuba🤣. Kowa dai da kallon mamaki ya bimu kawai. Su Aunty Mimi basu dad'eba sosai suka tafi, anbar laraba anan zata zauna damu. Samha da khaleel harda kukansu. ************** Bayan komawar su Galadima masarautane yakejin wai ba'aga Harun ba, k'ala bai tofa ba balle nuna alamun damuwa ko jimama. Saima shirinsa Na tafiya ya fara hankali kwance, yaje yayma mai martaba sallama. Suka wuce airport abinsu, dan jirgin 7:30pm zasubi.............✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻_* *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~BOOK 3~ 👉🏻7⃣ & 8⃣ ...............Galadima ya shigo murmushi d'auke a fuskarsa, dattijon dake zaune a falon ya d'ago ido yana kallonsa shima fuskarsa d'auke da murmushin, k'arawa Galadima yayi garesa, ya zauna kusa dashi yana fad'in “Baffina kanata jirana ko?”. Kafad'arsa dattijon ya dafa, yace “karka damu d'an baffinsa, nasan aiki mai muhimmanci ne ya tsaidaka. ya k'ok'ari?”. “Alhmdllh baffi, munata fama”. “ALLAH ya dafa mana, yanzu ina shi Darma?”. “Gashi a waje tareda ma'aikata, zamu jira zuwan Sir Isa ne, dan asan miya kamata, bazai yuwu mu had'ashi da su Harun ba”. “Uhm hakan shine dai-dai kam, amma yakamata suma bayanansu kagama tattarasu waje d'aya ka kawomin, kasan abubuwa zasu cud'e mana a tsakaninnan, dan fatana insha ALLAH wannan shine case Na k'arshe dazan fuskanta a rayuwar aikina, shekara 1 kacal ya ragemin cika talatin a matsayin lauya, insha ALLAH kuma zan cikasune bisa alk'awarin gurfanar da dukkan mai hannu akan mai martaba”. Murmushi Galadima yay, idonsa cike da kwalla, ya had'iye Abu mai d'aci yana fad'in “ALLAH ya cika maka wannan buri baffi, lallai ina alfahari dakai amatsayin uba, Kaine ka nunamin hanya alokacin da k'ofa ta rufe min, Kaine ka tsallakar dani a lokacin da gada ta karye ina tsaka da tafiya, ga kuma gagarumin hadad'i mai cike da tarnak'in iska ya taso, badan kaid'in ba da jajircewarka da yanzu ruwan daya zuba ya shafe da tarihina dana ahalina, da ace wani zai saurari labarina saiya d'auka labarin film ne ko novel, ni karan kaina nakanyi zaman yin tunanin anya akwai mai irin rayuwata a k'asarnan? Dan mafi yawa a tatsuniyoyi da hikayoyi akejinsa, saikuma abin mamaki ga nawa a zahiri, a yankin k'asar hausa, yanki mai tsananin ruk'on addini da Al'ada, yanki mai mutunta ahali da zuminci, inhar a shekaru 26 baya za'a iya samun masu irin ayyukan su tanderu lallai akwai abin tsoro kenan a k'arni nagaba da y'ay'anmu zasu mu'amulanta, Baffi da ace d'an Adam Na iya za6ama kansa rayuwa da banzo cikin ahalin jinin sarauta ba, amma Alhmdllh, ina godiya da Ubangiji daya halicceni yakuma San cancantar fitowa daga cikinsu.......”. kukane ya sark'e Galadima, Baffi ya mik'a masa handkerchief yana girgiza masa kai alamar kar yayi. Murmushin takaici Galadima yayi, sannan ya kar6a handkerchief d'in ya tsane k'ananun hawayensa. Baffi yace, “Muhammad Sameer akwai labarai da tarihin mutanen da yafi naka sark'ak'iya da hargitsi wlhy, sometimes abinda mukan gani a films ko hikayoyin marubuta akwaishi azahiri, saidai inhar bai faru akanka ba ko waninka saikaga tamkar k'anzon kuregene, kasan su mutane sunfi amfani da abinda suka gani da ido wato zahiri, ko suka San Wanda ya Sani wato tabbaci, a shekarun da nayi INA aiki nahad'u da cases da dama masu sark'ak'iya da ban tsoro, nakuma halarci kotuna da Dama domin ganin wasu cases d'in, idan ka samu wani case kai kanka saika ringa kokwanton anya kuwa wannan da gaske ya faru d'in? Amma daka tsananta bincikema saikaga abinda yafi Na farko mamaki, lallai a ranar gobe kiyama wasu zasu kasance cikin bayi masu tsananin kunyata agaban Ubangiji, Dan wata shari'a Ubangijine kawai mai iya mata, mu kammu acikin lauyoyi da alk'alai hummmm”. Baffi ya d'an bubbuga kafad'ar Galadima yana murmushi cikin takaici. Bai samu damar k'arasa magana ba akayi sallama, izinin shigowa ya bada, wani matashin dattijo da shekarunsa bazasu gaza 45 ba ya shigo, baikai girman baffi ba, sannan ya girmi Galadima sosai. Mik'ewa Galadima yayi yay salute nashi, dattijo ya murmusa yana kama hannun Galadima ya zaunar da fad'in “ni da kai adai bincika mai sarama wani”. Baffi yay dariya, “kudai kuka Sani da gardamarku wacce kullum bata k'arewa inhar kun had'u”. Bak'o mai amsa Sir Isa yace, “wai Yaya naga alhaji Rabilu zaune a waje suna sa'insa da banzan can?”. Nanma dai baffi ne Yakuma darawa, yace, “duk cikin aikine, dukkan wata magana dazai takalesa ya fad'a ai itama hujjace, kasanfa halin Alhaji Rabilu ai, shiyyasa nace masa da irin aikinku ya dace ba siyasa ba”. Sir Isa da yay dariya shima, yayinda Galadima ke murmushi, “Ai yalla6ai yanzu ma aikin dayake mana bashi da banbanci damu d'in, danya bamu damar sanin abinda tsawon shekaru muketa wahala da kaikawon sani”. “Wannan gaskiyane kam Isa, yanzu Yaya za'ayi da Darma kenan?”. Sir Isa ya gyara zamansa, yana saka d'an yatsa a baki alamar tunani, zuwa can yace, “inaga kam saidai mu nema wajen ajiyesa ko yalla6ai ya Adana mana shi, dan yakamata saimun kammala tattara komai a hannunmu bayan yalla6ai Galadiman mu ya dunk'ule kifaye a ragaya, idan sun mik'a wuya shima sai a sakashi a ayari ko?”. Baffi yace, “shawararka tayi kam, inaga yanzu abinda kasaba za'ayi, dan aiki da ilimi yafi aiki da agogo, kaike 6oyewa, kuma kaine akesa kanemo 6oyayye”. Murmushi Galadima ya sakeyi baice komaiba sai jinjina kai. Duk d'insu basu damuba, dan sunsan halinsa Na rashin son hayaniya tuni, ayanzuma suna d'an ganin canji fiye da shekarun baya, shiyyasa suka fara zargin ko (Hikimar matace take aiki?) Dan kad'an daga aikin mace ta tada gari, kuma kad'an daga aikin ta ta gyarashi. Sund'an tattauna har baba Rabilu shima ya shigo, wayar dayay recoding d'in dukkan musayar yawunsa da SD yabasu, babu Wanda baimasa jinjina ba, Galadima ya d'ora da musu godiyar hidimar da sukeyi a kansa tsawon lokaci. Suka amsa da cewar lallai mahaifinsa ya cancanci sumasa fiyema da hakan, dan yataka rawar gani shima a tasu rayuwar. Lokacin da suka fito abinda yabani mamaki shine su Ameer duk salute nasu sukayi suna k'amewa. Galadima basarwa yay, sai Sir Isa ne yay musu inkiyar su sauke hannayensu, baffi yay murmushi yana kallon Galadima dayak'i kallon kowa ta gefen ido. Sarkin mota dai yasha jinin jikinsa, musamman Basarwar da yaga Galadima yayi. SD dake zaune ya zuba tagumi yana kallonsu kawai ya janye hannunsa, cikin jinjina kai yace, “lallai duniya tana cike da abin tsoro, wai Isa kana nufin kaima wani abune a k'asarnan? Kai kuma babban munafuki Brr Usman Audu Tsanyawa! Ba kaine da kanka kaje kasamemu da albishir d'in ajiye aikiba? Ashe wannan k'aramin kwaron d'an cikinku kukema aiki?........” A tsawace Ameer ya katseshi, tareda d'aga hannu zai makeshi amma sai Galadima ya d'aga masa hannu. Sir Isa ne yay wata y'ar dariya yana matsawa ga Darma, yace, “Idan banda abunga Alhaji shehu kowama irin kune mai tsukakken tunani? Ai abin kallo bai k'are makaba saima nan gaba kad'an, kasan ita mota hanyarta kwaltace, birji ma idan tasamu bitake, balle dagwalon ruwa mai kayan datti, shikam jirgi miye gamisa da wannan? ko d'aga a tashi hanyar babu duk wad'annan, kaga kenan aikwai matuk'ar tazarar banbanci a tsakaninsu, kallon idoma tattancewa yake basai an shiga gasar tabbatarwa ba, kaikuma ai taka ta k'are, sauran shekaru sai a prison d'in dajin SAMBISA zaka idasu”. Dariya SD yayi, ya mik'e tsaye yana fad'in “iyaka dai Ku kaini police station, ina mai muku alwashin kwana d'aya bazanyiba a can, daga can a mik'amu Court, alk'alinma namune masu k'ananun basira, yanzu haka nasan sak'ona ya Isa ga y'an uwana, kafinma Ku kaini station d'in reshe ya juye da mujiya, dan dolene a kamaku da alhakin kamani kunga martabar wasu saita zube, mulkin da akema mutane homa da buri babushi kenan”. Murmushi Galadima yayi, dan yasan dashi yake, yad'an ta6e bakinsa yana cigaba da latsa waya hankalinsa kwance, Sir Isa da baffi da baba Rabilu, su Ameer duk kallon Galadima sukayi, don suji amsar dazai bada, amma saiya basar tamkarma baijiba. Saida ya kammala abinda yakeyi yay kiran Nuren suka kammala magana sannan ya kalli SD yana murmushi, “Wannan lissafin naka fa ya birgeni Alhaji shehu, saidai albishir d'in dazan maka nima shine, duk wani kira dazakayi ko ayi maka to zai shigo wayatane, yanzu haka driver d'inka yayi had'ari, rashin ganinka a motar kuma zantuka sun baje kowacce kafar yad'a labarai, Na tabbata dukkan labaran rana kaine shafin farko, hakama jaridun gobe masu fita, labarin nemanka da ta Yaya ka 6ata? Shine babban labari, sukuma abokan naka hakan zai tada hankalinsu, saisu fara zargin ko dai d'an tsohon Sarkine Galadima Sameer da wannan aiki?, dole kuma sufara bincike, bayan sun haukata y'an sanda wajen nemanka, daga haka kaga nikuma saina cigaba da samun hujjoji........🤦🏻 kai zaka samin ciwon kai wlhy”. Galadima ya karashe maganar da bud'e mota ya shige abinsa. Su Ameer duk suka shiga k'yark'yala dariya, saboda yanda Darma ya mugun shiga rud'ani da sakin baki yana bin Galadima da kallo harya shige mota. basu tsagaitaba saida Sir Isa ya tsaidasu ta hanyar d'aga musu hannu, yace, “Alahaji Shehu yadai? Kaji irin aikin masu basira ko? Kai! Kai! Harna tausaya muku lallai. Ameer! Kubi yalla6ai Galadima dashi, shikeda masaukinsa”. Angama ranka ya dad'e. Suka fad'a suna salute nashi. 🤦🏻‍♀lallai nimafa yau nashiga ciwonkan Galadima, shin wane laujene cikin nad'i kuma dabamu saniba haka? Nadai fahimci Su Ameer ba y'an iskan matasa bane, kamarma jami'an tsarone?🙆🏽. To Aunty Salama fa? Data kawosu a cakwakiyar. Masu karatu, kumuje zuwa dai, nasan komai yana gab da bayyana lallai kam.☹⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. __________________________ Galadima dai kam plaza suka koma, yayinda Nuren ya tari su Ameer a hanya suka bashi SD. Acikin Plaza Galadima yad'anyi zagaye-zagaye, saida ya tabbatar da komai dai-dai a wajen ma'aikatan sannan ya fito suka d'auki hanyar masarauta. ***************** Bayan fitar Galadima Aunty Mimi sashen su Munaya ta nufa, ta isketa har yanzu tana juya kalaman Galadima dabata fahimtaba. Bayan sun gaisa tabata Umarnin ta shirya dan za'a kaita sashen manyan gidan ta gaishesu da bangajiya sannan suga yara, inhar zaki tafi wanka bayan kwana d'aya da suna haka akeyi a masarautar, to amma su nasu Munaya yazo da Matsala, tunda gashi sai bayan kwanaki hud'u da suna zasu tafi, matan Sarkine kawai basa zuwa gida wanka. Kuyangi biyu sukaima Munaya shiri, itadai wannan lamari Na d'aure kanta, haka kawai da girmanka ace komai sai anmaka, dolene mai mulki yake kallon talaka ba komaiba, sauk'inta ma bakomaine Galadima ke bada fuskar ayi mataba, yama hana hadiman masarautar sakewa a sashensa gaba d'aya, sai iya wad'anda ya aminta dasu kawai. Yaukam tasha kallon kanta a mirror, hakan yakuma tabbatar mata da tuna mata agidanfa SARAUTA take, a kuma matsayin matar mutum mai girman rawani da matsayi a Masarautan. (Kusan dai mutuniyar taku da jan aji😉, ai saita kuma tsumewa tana basarwa🤣). Suma yaran an musu shirin dake nuna lallai Ubansu waninine a wannan masarauta, sannan suma ababen tattaline ga wannan kujera kwara 1 tal dakowa ke mutuwa da rayuwa a kanta a masarautar gagara badau☹. Sun sami rakkiyar kuyangi da Aunty Mimi, kowane sashe saida suka zagayashi amma a mota, an farane da fada. Yau itace ranar farko da Munaya ta shiga Fadar sarkin ta, yaukam taga abin mamaki, musalta yanda wannan fada ta k'awatu ai 6ata lokacine kawai, ammafa lallai komai yaji, ga Sarki hakimce bisa garagarsa cikin kwarjini irinna mutuntakar mulki, sarkinmu kenan kuma sirikinna ta wani fannini, daga ni sai aunty Mimi da kuyangi ukune muka shiga, kowanne d'auke da yaro d'aya a hannu. Fada cike take mak'il anata fadanci, Su Wanbai da talba duk ana ciki, hakimai da masu manyan muk'amai Na masarauta da wajen masarauta duk an hallara, kasancewar shine zaman farko Na wannan makon, kuma ana saka ran zuwan Governor ne da zaizoma mai martaba jajen abinda ya faru Na 6atan y'an uku, dan labarine daya zagaye kowacce kafa ta yad'a labarai da socia media Na k'asar nan, (kunsan dai abin manya duk k'ank'antarsa saiya fita, balle wannan da yazamo mai girma). Bayan Munaya da aunty Mimi sun zauna a k'asan lallausar darduma can gefe suka kwashi gaisuwa, dogarai suka amsa da yawun Sarki, sannan suka kuma gaisheda fadawa. Daga nanan aka amshi su Abdurrahman, y'an majalissar Sarki sukaita d'auka d'ai-d'ai suna saka musu albarka, da addu'ar fatan alkairi. Bayan fitowarsu sai sashin iyalan mai martaba, yau ma dai gimbiya zulfa bata fasa nunama Munaya da yaranta soyayyaba, daga Munaya har aunty Mimi basu San komaiba, dan haka sukaji dad'i da sakin jikinsu fiye da sauran matan sarki. Daga nanan sai sashen Mama Fulani, (kaga manya, Sarautar gagara badau a hannunku take, mama fulaninmu ta mutunci🤸🏻‍♀😂, ga irin naku manyan mata👍🏻) To kunsan dai mutuniyar taku, yauma dai cikin izzar mulkinta suka isketa, ita dama Aunty Mimi babu ruwanta, tana mata yanda takeso, shiyyasa babu y'ar habaici ko bak'ar magana tsakaninsu kamar Galadima, hakanne yasaka munaya samun tsira daga samun nata rabon, amma mama Fulani bata d'auki yaro ko d'aya ba, a hannun kuyangin ta gansu tana ta6e baki. Daga Munaya dai har aunty Mimi babu Wanda yay ko tari, to balle kuyangi dasuka zama takalmin takawarta, basu jimaba suka fito, haka sukaita zuwa sashe-sashe, basu sami Kansu ba saida suka Shiga ko ina . Sun dawo kusanda awanni biyu aka gama loda kayansu a mota Samha da Sauban suka shige gaba aka kai gidansu Munaya. Ita kuma sai zuwa yamma za'a mata rakiya. ************ Gidansu Munaya dai tunda kaya suka isa aka tsaya kallon-kallo, daga Sauban kam har Samha babu Wanda yamusu kallon arzik'i, yo sunaji da hayak'in girma dana mulki, innarsu Munaya da Munubiya da tuni tana gida kawai suka kula, harda sakin jiki dasu sukaita hira, sunmayi zamansu anan sai ankawo Munaya zasu koma. Nanfa matan gidan suka fara k'ananun magana, saidai babu mai yunk'urin d'aga murya saboda tsaro🤣. Oho innarsu Munu ma batasan sunayiba, balle Munubiya da yanzu saita ma gadama suke ganinta, ko yaushe tana d'akinsu, da anyi magana tace jego, dukda gasu Fiddausi a gidan duk suna wankan suma, Fauziyyace kan shigo susha hirarsu ta zuminci, amma sauran saidai idan an had'u a gaisa, kowa uwarsa Na kitsa masa munafurci a d'aki (🤦🏻‍♀gaskiya iyaye mata munada gyara babba ta wannan fannin, inhar zaka rayu gidan yawa sai kayi gamo da irin wad'annan matsalolin kuwa, ALLAH ya ganar damu baki d'aya dai). ****************** Su gadima Na shigowa masarauta ana kiran salla, hakanne ya sakasu yada zango a massalaci, saida aka idar sannan suka k'arasa sashensa, Duk agajiye yake, d'akinsa daret ya nufa, yashiga zame kayansa tun a falonsa, yana shiga ciki k'arasawa kawai yayi yashige bayi. Ya dad'e aciki kafin ya fito, baiko cire rigar wankanba yasha wani Magani ya kwanta, dan kansa ciwo yake masa. Cikin mintuna k'alilan barci yay gaba dashi. Munaya batasan ya dawoba, d'okin zuwa gida ya hanata barcin ranarma ita, sai yawan duba lokaci takeyi😂👍🏻. *_3:35pm_* Galadima ya tashi, saboda kiran wayarsa da akayi, idonsa a lumahe ya d'aga, a haka suka gaisa da Momma, ya tambayi Abie tace barci yakeyi, sunyi wayar kusan mintuna 15 haryaso makara fita sallar la'asar. Bayan yadawoma papi ya kira suka tattauna, sannan yakuma sabon shiri cikin Orange d'in yadi anmasa kwalliyar bak'i kad'an, yayi k'yau sosai, sai tashin k'amshi yakeyi, saidai fusakar kam babu alamun yasan miye dariya. A haka ya iso sashen Munaya, babu kowa daga ita sai yaranta da Khaleel dake barci a gefensu, itako wayama take latsawa, da alama game takeyi Kodai wani Abu. Sallamarsa ciki-ciki da k'amshin turarensa ya sakata d'ago ido suka kalli juna, yawani Basar yana shan k'amshi, hakanne yasaka Munaya sake kama kanta, ta gaisheshi, sau d'aya ya amsa ya zauna a bakin gadon yana shafa kan yaran d'ai-d'ai harda Khaleel. Handbag d'inta da mayafi dake ajiye alamar lokaci take jira kawai ya kalla, baki ya ta6e ya d'auke kai. Key d'in mota guda biyu ya fiddo a aljihu ya jefa min akan cinya. Ni harma Na tsorata na kalli keys d'in sannan Na d'ago na kallesa. d'auke Kansa yay daga inda nake, cike da k'asaitarnan tasa yace, bak'in kibama Abba, d'ayan kuma ki ajiye a wajenki, motar tana can, saboda ko wani abu yataso musamman kai yara asibiti sai wani ya kaiki cikin yayyenki, ki kulamin da yara, kuskure d'aya kikayi a kansu zand'au mataki mai tsaurine, duk abinda zuciyarki batayi na'am dashiba ki gaggauta kirana na sani, ki kula da Abdurraheem sosai, banda barinsa yana dogon kuka saboda doctor ya sanar mana yana d'auke da ciwon......”. Saikuma yay shiru yana furzar da iskar bakinsa. Masifar tsura masa ido nayi zuciyata Na bugu tamkar zata fad'o dan tsoro, sai tsuma nakeyi, babu shiri na taso na dawo inda yake, durk'ushewa nayi gabansa tamkar mai neman gafara, “Yalla6ai ciwon mi? Please ka k'arasa fad'an dan ALLAH”. lumshe idanunsa yayi yana cizar lips, “Ba abin tada hankali baneba ai, domin ALLAH daya d'ora mana yafimu sanin hikimar hakan, bagashi ni nakai lokacin da Magauta basuyi tunaniba”. Maganganunsa ya nuna minta cewar Abduraheem Na d'auke da Ciwon zuciya? kenan shima yayo gadon mahaifinsa?”. Matsowa nayi na fad'a jikinsa na sanya kuka, bashida za6i saina kar6ata shima ya rungumeni cikin yima Ubangiji tasbihin Neman dauriya da kar6ar jarabawa a duk yanda tazo. Bai hanani kukanba saida nayi mai isarta sannan na share hawayenna. d'agowa nayi daga jikinsa zan tashi amma saiya hanani hakan, cikin kunnenna yace, “Baki da kunya gaskiya, ban ta6a ganin uwa mara kawaici akan y'ay'an fariba saike”. Kunyace ta kamani, na 6oye kaina a jikinsa ina murmushi. Galadima ma murmushin yake yana shafa bayanta. Sun dad'e a haka sannan na tashi daga jikin nasa gudun kar khalel ya farka ya ganmu a haka, shima ya fahimceni, dan haka bai hanani ba. Yace, “Addu'arki yake buk'ata da taka tsantsan, dukda ba wayonmune zai hana Ubangiji ikonsa ba idan yaso, sai yakai watanni 6 zai fara ganin doctor insha ALLAH, ya mik'a mamin ATM d'insa, ga wannan dukdai abinda yataso saiki cira, amma a bimin kud'i a sannu ni talakane mai yawan buk'atu, ga Abdurraheem ya k'aru shima, to idan bawa bai nema kud'iba ai yagama shiga uku a wannan zamanin daba kowa ya damu da damuwarka ba, inadai kuma gargad'inki ki kula min da yara, yau zamu koma India, amma kwanaki uku zanyi insha ALLAH na dawo”. Nace, “ALLAH yabashi lafiya da dukkan al'ummar ANNABI, nagode sosai, saidai kuma inason kawai idan na tafi shi.......” Hannu ya d'aga min, “karki damu nasan maganar Aurenmu ne, kamar yanda na alk'awarin inhar komai ya fito kan shekara zamu rabu, inkuma ba a samu yanda akesoba shekara biyu inakan Sani, sauran bayani kibani lokaci zuwa kammala abinda ke gabana OK?”. ‘yay maganar yana kallonna’. Kaina kawai na d'aga masa ina had'iye abinda ya tokare mak'oshinna. Bai sake cewa komaiba ya mik'e yana kallon agogon hannunsa bak'i, “ku fito”. yafad'a yana ficewarsa. Da kallo kawai nabisa idonna yana cika da k'wallan dabasan na minene ba. ************** Munaya tasamu rakkiyar wasu daga masarautar, bisaga jagorancin Galadima da suke zaune a mota d'aya, daga ita har shi babu Wanda ya tankama wani koya kalli wani, shi tundama suka fito latse-latsen System yakeyi hankalinsa kwance, itama ta basar gefe tana kallon waje dukda glass d'in mai duhune. Sun Isa k'ofar gidan k'arfe 5:24pm, bayan su Aunty Mimi sun fita duk suka shige cikin gidan tareda Kuyangi. Munaya tayi yunk'urin fita amma sai taji motar a kulle, Sarkin Mota ta kalla sai taga harya fice, ta dawo da kallonta ga Galadima daketa aikinsa tamkar ya manta a mota yake. Shareshi nayi kamar nima bazanyi magana ba kamar yanda ya basar, amma saina kasa, na kuma kallonsa murya a sanyaye nace, “ka bud'emin mana, miye ma'anar zaman namu? Wanima saiya zargi wani Abu ai?”. Banza yay mani tamkar bazai tankaba, kusan mintuna biyu sannan yace, “idan sun zarga laifine? Naga Sadaki na biya”. “Hummm”. Munaya ta fad'a kawai tana d'auke kai. Saida ya gama shan k'amshinsa sannan ya ajiye lap-top d'in gaban motar yana matsoni. da mamaki na kallesa, “yalla6ai lafiya?”. “ita ta kawo haka”. ‘yafad'a yana wani ciccijewa da jawoni jikinsa’. Tamkar zan tsala kuka haka naji, dan naji zafi, mukaima juna kallon ido cikin ido, idona da kwalla tafara taruwa sai wani marmar yakeyi, matso da fuskarta yay sosai, cikin magana rad'a yace, “kin fara kewata ne?”. Baya naja da kaina ina tura baki da yamutse fuska, amma sai hannunsa daya sa ya tokareni ya dakatar dani daga matsawar, yakuma matsowa gaf, numfashin junanslmu na sauka a fusakar juna, a hankali yafara hura min iskar bakinsa saman ido, babu shiri na lumshesu, hawayen da suka taru suka zubo, sai kawai ya shiga sumbata ta. Tuni nabashi had'inkai babu wani gardama, saida yay yanda yakeso da ni sannan kowa yakoma gefe, wata y'ar k'aramar souvenir bag ya d'ora mani a cinya, sannan ya cire luck d'in motar, saida naja wasu Seconds nasamu dai-daita sannan ta bud'e na fice rik'eda bag d'in daya bani, ban yarda nasake koda kallonsa ba. Shima harta fice bai kuma kallon nata ba. Jiki a sanyaye nashiga gidan, matan gidanmu duk suna falon innarmu gaida bak'i, ina shiga muka rungume juna nida Munubiya muna hawayen da ita Munubiya tana tayani ne, nikuma bansan dalilin yinsuba🤣. Kowa dai da kallon mamaki ya bimu kawai. Su Aunty Mimi basu dad'eba sosai suka tafi, anbar laraba anan zata zauna damu. Samha da khaleel harda kukansu. ************** Bayan komawar su Galadima masarautane yakejin wai ba'aga Harun ba, k'ala bai tofa ba balle nuna alamun damuwa ko jimama. Saima shirinsa Na tafiya ya fara hankali kwance, yaje yayma mai martaba sallama. Suka wuce airport abinsu, dan jirgin 7:30pm zasubi.............✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻_* *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻7⃣➖8⃣ ..................Momma tayi farin cikin dawowar yaranta da jikoki, hakama Abie, wanda su Galadima sukai matuk'ar rikicewa da murnar ganin cigaban jikinsa, babu wanda baiyi hawayen farin cikiba, nanfa su Samha suka shiga nunama Momma da Abie hotunan yara da Munaya, Abie dake murmushi ya kalli Galadima da shima yake zaune ya hard'e hannaye a k'irji yana kallonsu da Murmushin, da ido Abie yamasa magana ya matso gareshi. Galadima ya tashi daga inda yake ya matsa kusada gadon, Aunty Mimi tabashi kujera ya zauna, hannunsa ya saka cikin na Abie yana d'an matsa masa, ada komi zakayi awani sashe Na jikinsa bayajin komai, koda zakaita dukansane bazaijiba, amma wannan hannun da aka samu canji da k'afarsa d'aya yanzu ko Yaya aka ta6asu saiyaji, yanda Galadima yake matsa masa hannun a hankali sai yakeji tamkar tausa, yad'an lumshe idonsa cikin jin dad'i yace, “ALLAH yay muku albarka gaba d'aya Muh'd Sameer, Na taya kaina farin cikin samun jikoki a tsatsona biyu, nakuma tayaka murna da samun y'ay'a a karo Na farko, bazan 6oye makaba ina k'aunar matarka, ina jinta a jikina tamkar kud'innan, tun randa Na fara ganinta ALLAH ya samin k'aunarta amatsayin d'iya, ina fatan ALLAH ya cigaba da saka albarka a cikin aurenku, ALLAH ya d'orar dashi har mutuwa”. Babu abinda zuciyar Galadima take sai lugude, auren dake gab da tsinkewa akema wannan doguwar addu'ar? Shikam yaga ta Kans....... Girgiza hannunsa Abie yay ganin ya fad'a duniyar tunani, ya sauke ajiyar zuciya yana murmushin yak'e da fad'in Amin akan la66a. Sun jima a haka Abie nata masa hira, kunsan dai halin mutumin naku, saidai yayta zuba murmushi, inda ya dace ya bada amsa kuma ya bayar, sun dad'e a asibitin kafin su koma gida, amma su aunty Mimi sun riga Galadima tafiya, danshi saida yaje Asibitin su namasu ciyon zuciya yaga likitansa, saboda a tsakaninnan dauriya kawai yakeyi, amma bayajin dad'in jikinsa. Duk wani abinda ya kamata Doctor Subash yamasa, Yakuma k'ara masa da Shawarwari. Lokacin daya iso gida har Samha ta gyara masa samansa da taimakon Sauban, ko ina yayi fes, dama suna sauka asibiti suka wuce, saboda d'okin son ganin jikin Abie. Ya fara zame kayansa idonsa bisa Sofa, ya lumshe ido yana cizar lips d'insa, bai kuma kallon sofar ba ya shige bayi, acanma dai bata sauya zaniba, dukkan abinda Munaya ta ajiye Na amfaninta irin Na mata idonsa Na wajen, haka dai yay wankan ya fito yana goge fuskarsa, sallar zuhur yafara gabatarwa sannan yadawo bakin gado ya zauna, wayarsa ya had'a, ya maida dukkan layikansa Na k'asar aciki. Knocking k'ofa da akayine ya sakashi kallon k'ofar, batare daya tankaba ya d'auke kai, aka kuma knocking, gutun tsaki yayi kafin yabada izinin shigowa. Samha ce d'auke da babban tire, kallo d'aya tamasa ta d'auke kai saboda ganin yanda ya d'aure. itadai ta ajiye ta lalla6a ta fice abinta. Yaja wasu adadin mintuna kafin ya mik'e zuwa wajen abincin, bubbud'ewa kawai yayi, yad'an ta6e baki yana rufewa, sai yama fice daga d'akin gaba d'aya zuwa d'akinsa na sirri. Komai yana nan yanda yabar kayansa, sai y'ar k'urar daba'a rasaba, amma dukda haka saiyaji yana k'yank'yamin d'akin, fita yay ya sauka k'asa, babu kowa a falon, da alama kowannensu gajiya ta kadashi, tsayawa yay yana tunanin wama zai tado? idonsa ya tsaya d'akin Sauban, can ya nufa, Sauban na kwance a gado yana danna lap-top Galadima ya Shiga da sallama ciki-ciki, tashi yay zaune da sauri, “Yaya Sam lafiya dai?”. “Shi wancan d'akin laifin mi yamuku dabaku gyarashi ba?”. Sauban ya marairaice kalar tausayi “ALLAH yaa Sam bayana ciwo, duk mun gajine”. Hararsa yayi, yana masa nuni da k'ofa, ya juya yay ficewarsa. Sauban yad'an tura baki yana sakkowa a gadon kamar zaiyi kuka, cik'in k'unk'uni yace, “shi Yaa Sam d'inna yanda yake aiki kamar wani ingi baya gajiya ya d'auka kowama haka yake”. Sanda ya fito har Galadima ya koma sama, shima hawan yay yanata kunkuninsa, a falo ya iskeshi zaune ya zubama wata kujera ido, baiyi maganaba ya shige d'akin, saida ya Shiga sannan ya Sanya dariya, dan ya kula kujerar da Munaya ke yawan zamace Galadima yakema kallon har hanji😂. Tsaf ya gyara ko'ina sannan ya fito, yanzu kam a kwance ya iskesa ido a lumshe, yace, “yaya Everything is done”. Hannu kawai ya d'aga masa, Sauban ya wuce abinsa, saida ya sauka ya juya ya kalli benen yana fad'i “Chiii yaa Sam He is too stubborn wlhy”. Aunty Mimi dake bayansa bai saniba tai dariya, “kadage ya jika dai, kasan ko kurar wasa saita fika gata agidannan”. Juyowa Sauban yay ya kalli aunty Mimi yana dariya shima, “Aunty babba ai lamarin boss ne sai addu'a” ya matso kusa da ita yana rage murya alamar gulma, “kinsan mineme kuwa?”. Kanta ta girgiza masa. Yacigaba da fad'in “Wlhy Ku taimakemu Ku amso masa matarsa da wuri, dan yafara rikid'ewa zai koma asalin Muhammad Sameer d'insa saboda kewarta”. Idanu Aunty Mimi ta zaro waje, cikin sakin baki da tafa hannaye tace, “Sauban! Yaushe ka fara sanya masa ido?”. Dariya Sauban ya tuntsure da ita ya shafa kansa yana fad'in “Aunty jeki sama kisha kallo mana”. ya shige d'akinsa yana cigaba da dariyarsa. Itama dariyar tayi, a fili tace, “Munaya kin biyamu wlhy, ALLAH ya bamu ikon miki halacci kema fiye da wanda kikai mana”. Nane, “amin waunti mimi😄”. )*()*()*()*()*()*()*()*()*()*()*( To yau dai ga Munaya ga Munubiya a gida, gaban innarsu, ga y'an k'annensu, abin sha'awar harda k'arin y'ay'ansu, ita kanta Innarsu kallo d'aya zai tabbatar maka da farin cikin datake a ciki, badan aureba mixai rabata da y'an y'ay'anta masu tausayinta. Ranar dai haka muka kusan kwana hira da labaran yaushe gamo, kota yaranma bamayi sai laraba ce da innarmu kemana magana akan mu shayar dasu. Washe garima mun tashi cikin farin cikin kasancewa da juna, aka dama mana kunun kanwa mai rai da lafiya, yanata k'amshin kayan yaji, ga k'osai mai dad'i a gefe, munacin kayanmu muna hira, Fauziyya ta shigo itama tsaf da ita, jegon ya kar6eta sosai, rungume juna mukayi ni da ita cikin kewa, itama ta zauna muka cigaba da karin kumallon tare, anan take bamu labarin wahalar datasha wajen haihuwa, yanzu hakama ita ba'a mata wankan jegon, saboda jininta yak'i sauka, sosai Muka tausaya mata, da fatan samun lafiya a gareta, nace muma ai munsha wahalar, nabasu labarin nak'udar kwana uku danasha kafin mu taho Nigeria, Munubiya harda hawayenta, dukda itama tasha tata azabar. Inna dai da Laraba najinsu daga tsohon d'akin su Munayar suna musu dariya, sunsha hirarsu har d'agawar hantsi, saida aka aiko kiran Fauziyya yaronta Na kuka sannan tamik'e ta tafi. A sannan ne Innaro ta shigo gidan, dama kullum takanzo taga masu jegon, d'akin kowa ta shiga taga sauran, Dan ita Safara'u ma takusa komawa, tunda itace ta fara haihuwa itada Haleematu. Ni da Munubiya muka gaida Innaro, amsa muna tayi babu yabo babu fallasa, hakkane ya sakani shareta nacigaba da latsa wayar Munubiya da ke hannuna. Innarmu ta fito daga d'aki d'auke da Abdurraheem daya farka yana kuka. Innaro ta wani bud'e baki da rik'e ha6a tana kalon innarmu, cikin tafa hannaye tace, “O ni Marwanatu, yanzu nan Ai'sha jikan farinne kike mamuk'a haka tamkar wani autanki?”. Kallon juna Mukayi ni da Munubiya, sannan muka kalli innaro, ganin Innarmu ta tsaya sororo alamar tad'anji kunya sai Munubiya ta mik'e, inda take taje ta amsa Abdurraheem d'in. “la'ilahailllahu..”. Innaro tafad'a cikin mik'ewa a zabure alamar mamaki, tace, “A lallai duniya tazo k'arshe, ke kinmafi uwar taku ashe? Dagani babu tambaya nasan Munaya ce wannan, fetsararriya anzo a d'ora daga inda aka tsaya kenan?”. Murmushi nayi, Na kar6i Abdurraheem da Munubiya ta d'oramin a cinya, saida Na fara shayar dashi sannan Na kalli innaro, nace, “Innaro inhar kin shirya d'orawa daga inda kika tsaya muje zuwa mana, indai bazaki canjaba Munaya ma har abada zabata canjaba, miye laifin Innarmu danta d'akkoshi yana kuka?, rawa kika tarar tana masa ko wata tsiya? Yo nagama kema haka kikaita ma mutane kuka saikinje jiyyar abbanmu India, halan kema kunyar d'an farince.......”. Bankai k'arshen zancenba innaro ta d'ora hannu bisa ka ta aza mana kuka. Ni da Munubiya muka kuwa kwashe da dariya abinmu, a haka abbanmu ya shigo ya samemu, Innarmu tanata bama innaro hak'uri tak'i saurarenta. Girgiza kai kawai Abba yayi, Dan akan idonsa komi ya faru, hannu ya d'agama Innarmu alamar ta barta, zata fara magana ya girgiza mata kai. Shiru tayi takoma gefe, innaro saita k'ara k'arfin kukanta wanda harya fara jawo hankalin matan gidanmu, saidai babu damar zuwa kallon kwaf tunda a d'akine. Hannun innaro Abba ya kama ya zaunar da ita, cikin kwantar da harshe yace, “haba dai inna, yanzu dan ALLAH abinda akayi yarannan Na k'anana yanzuma shi za'a sake azaman dazasuyi Na wata 1 kacal dawasu kwanaki? Haba inna, minene Dan yaro yayi kuka Ai'sha ta d'akkoshi? Inna ina dad'i irin wad'annan abubuwan haka?”. Share hawaye innaro tayi, tace, “to naji Auwalu, indai nice bazan sake magana akan y'ay'anka da matarka ba....”. “da yafi”. Nafad'a ina murgud'a baki. Hararata Abba da Innarmu sukayi, Abba ya rik'e hannun innaro da sauri saboda k'ok'arin tashi da takeyi, “kiyi hak'uri Dan ALLAH inna, niba haka nake nufiba, da ni da abinda Na mallaka ai duk mallakinkine, nafad'a ne dan kawai a zauna lafiya yarannan sugama wanka kowa takoma gidan mijinta cikin salama, tunda kinga dai da yaran d'akinnan ne kawai irin wannan sa6anin ke shiga, yanzufa kika fito d'akin can kina tsokanar yarinyar Haleematu, mizaisa anan kuma hakan bazata kasanceba?”. “shikenan naji”. Abinda innaro tace kenan kawai ta mik'e ta fice. Abba ya bita da kallon kawai cike da takaici. Gaidashi mukayi, ya amsa yana had'iye 6acin ransa, ya tambayemu ya yara?, duk shiru mukayi muka kasa amsashi saboda kunya. Murmushi yayi, ya kar6i Abdurraheem daya gama shan nono, bayan Innarmu yabi d'akinta d'auke da yaron, dan tunda yamata magana tabar falon ta shige d'akinta. Zaune ya isketa a bakin gado tayi tagumi tana hawaye. Ya zauna kusada ita rungume da Abdurraheem, shiru yay yana kallonta, kusan mintuna biyu ya kwantar da yaron a bayansu yamatsa jikinta sosai yana kwantota jikinsa, “kiyi hak'uri Ai'sha, a halin inna babu wanda baki saniba yanzu, tunkan kizama mata a gareni kinsan wannan, to mizaisa hakan yasakaki kuka a yanzu? wani abin nata harda tsufa yanzu, amma kiyi hak'uri dan ALLAH”. “Ni ba kuka nakeyi saboda abinda inna takeminba, ina kukane saboda rashin jituwar da kullum take k'ara tasiri tsakaninta da yarannan, duk yanda naso hana girmamar irin wad'annan abubuwa n abun ya gagara, bai kamata ace laifina yana shafar jikokinta ba, jinintane fa su, idan ni tace banda asali sukuma ai itace asalinsu ko? wlhy Abbansu banason wad'annan abubuwan, wani lokacin zuciyata takan gaza d'auka”. “kiyi hak'uri, insha ALLAH komai mai wucewane, yakamata kuma zuwa yanzu kufad'a mana Ku su wanene? Kodan yaranki, dangin mahaifiya sunada matuk'ar tasiri a rayuwar yaro, banason zuwa nan gaba su zargi abinda ba haka yakeba, kodan gudun suma y'ay'ansu su taso suyi musu irin wannan tambayar”. Murmushin takaici inna tayi, ta d'ago daga jikinsa tana share hawayenta, suduka kallon Abdurraheem daketa motse-motse da k'afafu yana dungurin bayansu sukayi, Abba yay murmushi yana shafa kansa, sannan ya kalli inna yana fad'in “Ai'sha kodan wad'annan yaran, dolene watan watarana sai tarihinsu ya shafi tsokaci dangane da usilin mahaifiya, dukda nawa za'a kawo saifa naki ya taka rawar gani shima”. Inna tayi murmushi itama tana shafar kumatun Abdurraheem d'in, ta mik'e tsaye tana cewa “karka damu, a bani lokaci, da izinin ALLAH saisun taka tushena da k'afafunsu”. Abba ya d'auki Abdurraheem ya rungume yana fad'in “ALLAH ya tabbatar”. Mukan bamusan wainar da ake toyawaba, muna falo yara suna Neman haukatamu da kukansu, dukfa barci suke, amma Meena Na tashi kamar jira suma duk suka tashi masu kawunan kwakwar.😏 Haushi ya isheni nakusa make Amaturrahman datafi kowa daddagewa, saida Munubiya ta rik'e hannuna, “Sweetheart wai baki da hankaline? Uwarmi zaki daka ananne?”. Cikin tura baki nace, “yo Sweetheart haukatamu zasuyine?”. Daga inna har Abba dake fitowa baki suka gumtse suna dariya, “A lallai akwai aiki babba a gaban mata ashe?”. Inna tafad'a tana kallon Abba. Murmushi yayi shima yace, “babba kuwa Ai'sha”. Sai sukayi dariya. Hakanne yasakamu farga dasu, muka juyo muna kallonsu kowa fuska a tur6une, saboda haushin da yaran suka bamu. %%%%%%%%%%%%%%%% Bayan kammala gyara da Sauban yayi, Galadima ya mik'e zuwa cikin d'akin, zama yay ya kunna dukkan Computers d'in d'akin, saida komai ya dai-daita sannan yafara aikinsa cike da kwarewa, har lokacin sallar la'asar yana a d'akin, shiko gajiyar zaman jirginma bata damesa ba, bedroom d'insa ya dawo yay salla sannan ya sauka k'asa, Samha yabama Umarnin abinda yake buk'ata ya dawo yacigaba da aikinsa. Mintuna kad'an sai gata takawo masa. takan shiga shauk'i idan taga Uncle Sam yana sarrafa Computers d'innan, saitaji tamkar yafi kowa ilimin sarrafa Computer a duniya, amma tasan dole sai ansamu wanda suka fishi, badan karya maketa ba data tsaya taita kallonsa kawai. Shi baimasan tanayiba, hankalinsa nakan aikinsa gaba d'aya, dukda kansa daya fara ciwo kad'an-kad'an burinsa yakai inda yake hari. Saida duhun magriba ya gabato sannan yasamu kansa, yanzu ma a d'akin yay sallar magrib, ya zauna karatun Qur'an har time d'in isha'i yayi. Yana idarwa ya d'ora da shafa'i da wutiri, saboda barcin dake damunsa, soyake ya kwanta da wuri, duk abinda yakeyi kafin barci saida yay k'ok'arin kammalashi da k'yar sannan ya kwanta, dukda tunani da kewar yaransa Na neman 6atar da barcin nashi haka yayta yak'i da shi har barcin yaci Galadima akan tunanin. Samha tazo kawo masa dinner ta iske yanata barci cikin bargo, yama kashe hasken d'akin saina fitilar gefen gadon kawai itakuma haske kad'anne. Ajiye abincin tayi, dukda mawuyacine ya tashi domin cinsa, musamman da saida yamma yamaci d'azun.. (((+)))★(((+)))★(((+))) Yau kwananmu biyu kenan da dawowa gida, nayi waya dasu Samha duka amma banda uban gayya Galadima, bai nemini ba nima ban nemeshiba, Momma kam kullum sau biyu take kira muyi video call itada Abie, safe da yamma duk takan kirani. Muna kwance a gado ni da Munubiya, sai kuma mak'e murya takeyi suna waya itada yaa Marwan, koni dake kusa da ita ba komai nakejiba, nayi murmushin takaici ina juya kwanciyata zuwa d'ayan 6arin, danma Na daina jinta gaba d'aya, wata kwalla ta tararmin a ido, ba bak'in cikin kasancewar y'ar uwata a farin cikin nakeba, a', tausayin kainane ya kamani, maybe ita kad'aice zata koma gidan nata mijin banda ni, Na kalli yaranmu da laraba keta musu shirin barci, Aiyaan da Aryaan nata jagwalgwalasu, saurin d'auke k'ananun kwallar dake Neman zubomin nayi. Ni dai har barci ya d'aukeni bansan lokacin da Munubiya tagama wayarnanba, ban farkaba saida yaran suka farka da kuka, yanzu sabon iskancin da suka tsiro dashi kenan su duka 5 d'in, wato kukan dare, da zarar 2am tayi tamkar an kad'a musu k'ararrarwar tashine, haka zasuyita kuka har sai asubahi ta gabato sukeyin shiru, da zarar asuba tayi saisu hau barci, ko wankan safe za'a musu sai an tashesu, daganan wani sabon barcin suke d'orawa, haka zasu yini barci, sai dare yayi suce basusan zancenba. ALLAH yau tamkar namusu kuka haka naji, dama ga haushin Ubansu dana kwanta dashi, ficewata nayi daga d'akin nakoma falo Na kwanta, nabar Innarmu da Munubiya da laraba dasu. 🤣ho Munaya kad'anma kenan🤭. ////....//////.....//////....//// A kwanaki biyunnan gaba d'aya Galadima cikin kai kawo yayisu, bashi Company bashi wajejen daduk yake Business, bashi Asibiti wajen Abie, yanason ya killace komai wajen wad'anda zasu iya kula masa da Amana, saboda baisan iya adadin lokacin da zai d'auka a Nigeria ba wannan lokacin, inma zai shigo india bazai dinga wuce kwanaki biyuba zai barta, shima dan yadinga zagayo iyayensa ne. Har y'ar rama yayi saboda tsabar komawa busy, ga kewar yaransa (niko nace kodai harda uwar yaran🤣🥴). Momma kawai tasan halin da ake ciki, amma koda wasa basa sanarma Abie komai dangane da hakan, yakanyi dai mamakin komawar Galadima busy a wanan dawowar, dan ko asibiti yaje baya zaman 30minutes yake fitowa. Abie dai ya kasa hak'uri ya tambayi Momma, saita cemasa wani aikine zasuyi a Nigeria gameda Company d'insu, kuma shi aka d'ora akan aikin, shiyyasa yakeson tattara komai wajen mutanansa nanan. Abie yace, “to ALLAH ya taimaka, yabada nasara fiye da wanda ake tsammani”. Momma taji dad'in wannan addu'ar, dan haka ta amsa da “Amin” cike da fara'a. A kwana Na uku Galadima bai samu damar tafiyarba dai, saboda bai kammala uzirorinsa ba, dole ma zai k'ara koda kwana biyune. Sauban harda rawa dan dad'i, dan shifa bason zaman masarautar nan tasu yakeba🤥. Yauma a gajiye ya dawo gidan, kallo d'aya zaka masa ka fahimci hakan ko a yanayin tafiyarsane da fuskarsa datai cinkus babu walwala, hannu kawai ya d'agama su Samha dake falo suna gaidashi, harya 6acema ganinsu daga hawan benan idonsu Na kansa, tausayinsa ya kamasu, shidai yana shiga tun a falo yafara zame green jacket d'in dake saman kayansa, ya k'arasa cikin bedroom d'in yana jefa rigar saman sofa da furzar da huci, freight ya bud'e ya d'auki ruwa, batareda kofiba yahau shan kayansa, tas ya shanyeshi ya jefar da robar yana had'iye wanda ke gumtse a bakinsa, sannan ya k'arasa bakin gadon ya zauna ya dafe kansa, tsawon mintuna uku yana a haka shiru, har wayarsa tafara wringing amma bai kulaba, saida aka kira kusan sau uku sanannan yama kalli wayar yana k'aramin tsaki, kamar bazai d'agaba amma saiya d'auki wayar tana gab da tsinkewa, kafin yay picking call d'in ta tsinke. Kiransa yayi dan Nuren ne. Bugu d'aya Nuren ya d'aga, bayan sun gaisa yake sanar masa yarinyar minister ce batada lafiya, kuma ya lura yarinyar kamar tanada Asthma ma ne. “Asthma? to miye ya tada ciwon nata? naga dai ba wani Abu dazai iya shafar tashin ciwon nata a gidan?”. “hakane Brother, wlhy muma bamusan daliliba”. “Toni yanzu daka kirani mizan muku ina nan?, kufita ku nema mata magani mana”. “Muftahu ya tafi, dama na gaya maka ne ka Sani kawai”. “okay. ALLAH yabata lafiya to. Ya maganar Harun?”. “Sunan sun baza cigiyarsa gidajen redio shida Alhaji Darma, kaga yanda kuwa suka gama rikicewa, da farko sunce yayi Accident shida driver d'insa amma anrasa inda yake shi, to inaga ko driver n ya dawo hayyacinsa ne ya sanar musu shikad'ai yay Accident d'in oho, jiya dai saiga wata sanarwar suna fad'in anyi Garkuwa da shine tunkan accident d'in, amma har yanzu ba'a nemi kud'in fansaba, dan kidnappers d'in basuce komaiba”. Galadima yay murmushin gefen baki yana susar gashin girarsa a hankali, yad'an cije lips yana fad'in “toko zaku saka kud'ine marayu su sami na abinci da kud'in makaranta”. Dariya Nuren ya kwashe dashi, yace, “dan ALLAH da gaske kake brother”. Kwanciya Galadima yayi yana fad'in, “kai d'an air wasa nakeyi”. Nuren yay kwafa, “wlhy da ace gaske kakeyi Kansan ALLAH saina k'ure dukiyarsa sannan, nakuma rud'asu da cewar ya fad'amin wani sirri, idan basu biyaba zan tona”. “ALLAH ya shiryeka to”. Galadima yafad'a yana kuma tashi zaune. “Amin”. Nuren ya amsa. “Wai anya kuwa zaka shigo yau d'in?”. “No, maybe ma sai nanda kwana biyu ko uku, bangama hidimomina ba, kudai kuci gaba da kulawa...”. K'it ya yanke wayar batareda jiran abinda Nuren zai ceba. Takalminsa ya cire da kayan ya shiga wanka, yad'an jima sannan yafito d'aure da towel ya yafo wani a jikinsa, ya zauna saman sofa yana d'aukar wayarsa, number d'inta ya lalubo, sai kuma ya kasa kira ya kurama number ido kawai, tun randa suka iso hakanne ke faruwa, saiya d'auki wayar kamar zai kira saiya fasa, gashi yanason jin Yaya yaransa da jikin Abdurraheem, ya danna kiran yana cizar lips d'in nasa daya zame masa jiki🙄😏. _______________ Muna zaune a d'akin mu ni da Ayusher, Feena da sukazo, tirene a tsakkiyarmu munacin d'an wake da Maman yaa Hameed tayi yau dan aikintane, wayata na hannun Feena tana kallon pictures kiran ya shigo, kallona tayi ta kalli wayar ta kwashe da dariya tana mik'omin. Muduka kallonta mukayi da mamaki, na kar6i wayar ina fad'in, “kekam kokin fara zarewane?”. Bata bani amsaba, saima dariyarta take cigaba dayi, na kalli wayar nima, a dai-dai nan kiran ya tsinke, sunan mai kiranne ya d'auki hankalina, *_“Rabin raina!”_* na fad'a a saman lips, ni dai banyi saving number kowa hakaba, yanzu na fahimci abinda yabama Feena dariya kenan. Daga can Galadima yay tsaki, yana jefar da wayar ya mik'e zuwa gaban mirror, saidai kuma zuciyarsa takasa hak'ura, sukda haushin kansa da yakeji na kiranta da yayi, to amma ai dan yaransama yayi, shine zatak'i d'aga masa waya? zuciyarsa tace idan kuma bata kusafa? Kokuma yaran ne suka d'auke mata hankali da kuka. Iska ya furzo daga bakinsa, dan tuna hakan zata iya yuwuwa kuma, saiya mik'e ya d'auki wayar, lallai yau Munaya takafa tarihi a rayuwarsa, ko Momma idan yay mata kira d'aya bata d'agaba yakan hak'ura saita kirashi, inhar baya mantaba baita6a kiran mutum a jere sau biyu ba a rayuwarsa. kiranta ya kumayi yana wani ciccijewa fuska a murtuke, kai kace tana gabansa ne. Har yanzu ina cikin mamakin ina na samo sunan? kiran yakuma shigowa, yayinda feena take gayama su Munubiya abinda ta gani, tashinai daga wajen ina d'aga kiran saboda hayaniyarsu. Koda na d'aga sai akak'i magana, nima sai nayi shiru, ganin abin bana k'are bane nace, “Idan babu buk'atar magana ai banga dalilin kiraba”. Daga can Galadima yay murmushi yana shafa sajensa da kallon kansa a mirror, a ransa yace anan da hali dai. Har zan yanke sai akayi gyaran murya, tun a sannan na gane shine, na zaro ido cike da mamakin waye yaymin saving number haka? Lallai ko rantsuwa nayi babu kaffara, Samha ko Sauban. Galadima ya katseta da fad'in, “wannan tarbiyyar zaki bama yarana kenan na rashin iya gaida na gaba dasu?”. Dukda Naji haushin maganarsa amma naji kunya, nace, “To ba shiru kayiba kaima”. “naji to mai bakin tsiwa, gaisheni”. Nakula abin nasa harda tsokana, dan hakan nace, “ina kwana?”. Yace, “A 9ja ko?”. Tunawa nayi time d'inmu fa ba d'ayaba, sai nace “Ina yini”. Ya amsa da “lafiya. Ina abin cikin kwan?”. Kamar bazan amsaba saidai nace, “waye mai wannan sunan?”. Galadima ya murmusa yana cija lips, “karki damu kwanaki kad'an zakiji wasu ukun ko biyu a jikinki, daga nan saiki tuna mai sunan”. Da sauri nace, “can gasu gada, idanma hakan tafaru to sai dai ga masoyina mai zuwa, wanda yadamu dani, ina maka albishir nasamu mijin aure”. Murmushi Galadima yakeyi yana shafa kansa, yace, “Ayya natayaki murna gaskiya, sai dai shifa mijin ina tayashi jajen rashin iya za6e”. Wani haushine ya kamani, na yanke wayar ina tsaki. Dariya sosai ta kama Galadima, ya ajiye wayar yana fad'in “kujimin yarinya, ke kika kawo zance, miye kuma najin haushin?”. Ta6e baki yayi ya tashi zuwa gaban wardrobe yay shirin barci hankalinsa kwance. _____________ Tunda na yanke wayar sainaji kuka na Neman tahomin, amma na daure na danne abina, komawa nayi cikin d'akin na haye gado, Ayusher tamin magana akan nazo muci gaba dacin abincin amma nace na k'oshi, lallashina sukaitayi itada Feena, nak'i saurarensu, Munubiya kam uffan bata ceminba, hasalima ko kallon inda nake k'inyi tayi, dukda nasha jinin jikina akan haushina takeji saina shareta nima. Har dare muna tare dasu Ayusher, sai bayan isha'i Yaa Marwan yazo d'aukarsu, nafita kawo masa ruwa saboda na freight d'inmu ya cika sanyi, yace kuma bazaisha mai sanyiba, koda na dawo saina tarar basa nan shi da Munubiya, Ayusher tace, yace nakai masa d'akinmu. Ban kawo komai a rainaba na nufi d'akin cikin karsashina, saida naje tsakkiya sannan idona yay mugun gani, daga Munubiya har yaa Marwan da suka farga da shigowata suka d'ago kowanne ya zubamin harara. Babu shiru na dangwarar da ruwan a wajen nima ina murgud'a baki na fice abina............✍🏻 🤣Ya Marwan kamin dai-dai kaida Munubiya🤨 su o'e sai a canja hali, dan duniya saida kud'i lahira kuwa sai da hali🤸🏻‍♀, ko ya kukace my Guys😂😜?. *_Duk wanda yamin magana PC shekaran jiya yaga babu reply yamin afuwa, wayar tawace hawan madara ya kamata, sai kawai ta goge komai, shiyyasa nai zuciya jiya naki muku typing, dan nayi ya goge😢_* *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻9⃣➖🔟 ..............Kwana biyu Galadima ya k'ara suka dawo Nigeria shi da Sauban, burinsa a yanzu ya fuskanci abinda ke gabansa da iyakar k'arfinsa da basirarsa, bai shiga masarauta ba saida ya had'u da baffi yabashi wasu takardu. Dole yay barcin wasu awoyi domin samun nutsuwar gajiyar tafiya, sannan yay shirin fitowa, ya lek'a sashen mai martaba dansu gaisa saiya tarar yanada bak'o, jakadiya sarkin gulma ta gutsiri goronta tana kallon Galadima, “Ranka ya dad'e ai takawa yana tare da bak'one, bak'on kuma Na lura Wanda ba'ason sanin dami yazone, dan kullum ganawar sema k'unshe yakeyi da takawa”. Shiru yamata tamkar bai jiba, danshi mutumne da baya shiga abinda bai shafeshiba, kowa yasan haka a masarautar, shiyyasa Duk makircin masarauta bazaki ta6a samun wani ya sakoshiba, kokuma kawo masa gulmar wani. Ganin haka itama jakadiya sai taja bakinta tayi shiru. Galadima ya mik'e yana kallon agogon hannunsa, “Bara naje, zan dawo anjima”. ba tare da ya kalleta ba yay maganar yay kuma ficewarsa. Da kallon ta bishi tana cigaba da 6allar goronta, tace, “wannan murd'ad'd'en da ace zai saurara dana bashi sirrika da yawa wlhy, amma ina, maganama ta kud'ice a garesa, ka huta wlhy, wai gurgu ya za6i zaman waje d'aya😏”. 😂😂🤭 _______________________★ Kwance yake jikin seat d'in mota idonsa a lumshe, duk yanda yaso ture zancen jakadiya a ransa karyay tasiri ya gaza hakan, sai kaikawo zancen ke masa, tabbas bak'o mai muhimmanci ne kawai zai iya ganawa da mai martaba har cikin turakarsa, to mike faruwa ne haka?, bashida amsa dan haka ya cije lips d'insa, tafiyar tasu yau dagashi sai sarkin mota, ya hana dogaransa binsa, gidan da su Nuren suke ya isa, dukda shi Nuren ma baya nan yaje gida saboda kiran gaggawa da papi yamasa, Muftahu kam dole kullum a Masarauta yake kwana, saida taka tsantsan ma yake zuwa gidan da rana, saboda rashin ganin Harun yanzu motsin kowa lura akeyi dashi. Su Ameer ne suka bud'e musu k'ofa Sarkin mota ya shiga, yanayin parking suka bud'ema Galadima ya fito, cike da girmamawa suka gaisheshi, ya amsa musu da d'an sakin fuska, sannan ya tambayesu Yaya aiki?. Da Alhmdllh suka amsa. Har cikin falon sukai masa rakkiya, babu kowa cikinsa, amma ko ina k'al yake a gyare, ga k'amshi mai dad'i yana tashi. Yayi zama yakai Na 10minutes saiga baba Rabilu shida wani dattijo da zai iya girmarsa kad'an, kokuma wahalace ta girmamawa tsufan nashi oho. shidai Galadima kallon mutumin yake tamkar ya sanshi, amma ya manta a ina. Zama sukayi, cikin girmama juna suka gaisa, sukaima Galadima barka da dawowa, da d'an guntun murmushi ya amsa, har yanzu dai idonsa akan dattijonnan. Lura da hakan da baba Rabilu yayi saiya murmusa, yace, “Ranka ya dad'e ka shaidashi ne?”. Galadima ya hard'e k'afafunsa yana murmushi, yace, “baba rabilu inadai masa kallon Sani kam”. Baba Rabilu yay k'aramar dariya yana kallon dattijon dake durk'ushe a k'asa shima yana Murmushi, sannan ya dawo da kallonsa kan Galadima yace, “Zaka sansa Ranka ya dad'e, amma gaskiya kana tare da k'uruciya lokacin, Sunansa Badi, mahaifinsa shine mai kula da dawakan Sarki a wancan lokacin”. Da sauri Galadima ya sauke k'afafunsa daya hard'e, cikin tsantsar mamaki yace, “Baba Rabilu kana nufin wannan Badi ne?”. Dattijo ya risinar da kansa k'asa alamar girmamawa ga Galadima. Yace, “Nine ranka ya dad'e”. Rasama abinda Galadima zaice yayi. Sai bakinsane ke motsawa alamun yanason maganar amma ya kasa. Sai ido daya tsurama Badi cikeda tunosa a lokacin da shi yake d'an shekara 5 kacal a duniya, dukda bazai yuwu ya iya tuna komaiba, amma tabbas yasan fuskarsa, yasan kuma shine mai kulawa da barga ta dokunan masarautarsu shi da iyayensa, a lokacin inhar baiyi k'aryaba Badi bazai wuce shekaru 33 ko 35 ba. Amma yau gashi zaune gabansa furfura da girman tsufa duk sun bayyana a garesa...... Sallamar Muftahu ce ta katse tunanin galadima, Muftahu ya zauna suka gaisawa da Baba Rabilu, sannan ya gaida galadima, idonsa dai nakan Badi shima. da k'yar Galadima ya amsama Muftahu gaisuwarsa. Badi dakema muftahu kallon sani ya gaisheshi cike da girmamawa (Dan ALLAH yayisa mutum mai yawan rik'o). Muftahu dai kasa hak'uri yayi, ya kalli baba Rabilu yana neman amsa. Murmushi baba Rabilu yayi, ya gyara zamansa yana fad'in, “Yalla6ai baka ganesa bane?”. Muftahu yace, “Banma ta6a ganinsa ba alhaji”. Badi ya kalli Muftahu sannan yay k'asa da kai. Yace, “Nikuwa kaga Na ganeka yalla6ai, dan bazan manta sanda kukan rako Yarima ba idan za'a fita da shi bakin ruwa shan iska, ka kan nace sai a doki d'aya zaku tafi kai da sauran abokan nashi”. Murmushi Muftahu yayi, ya kalli Galadima dayay shiru yana kallon Badi kawai, yasan yana tuna bayane, kuma akwai tambayoyi fal ransa sai dai ya kasa furtawa, janye idonsa yayi ya maida ga Badi, yace, “Amma Badi minene ya faru da kai harka bar masarauta? dan bazan iya tuna wani abuba a wad'ancan shekarun namu, yanzu kuma daga ina kake?”. Zama Badi ya gyara. Yace, “lallai labarine mai tsawo da Nisan zango, amma a tak'aice dai abinda zan iya cewa shine.....”. _“Bayan kwanciyar mai martaba adalin sarkinmu jinyar da ba'asan mafarinta ba da wata biyu kacal ranar wata lahadi da tashin hantsi munje kasuwa ni da mahaifina mun sayo abincin dokuna mun dawo, muna tsaka da sauke kaya a barga saiga wani mutum a tsakkiyar harawar dokunan cikin a kori kurar da muke zubo kayan kenan, dagani har mahaifiyata da mahaifina mun razana matuk'a, harma k'anwata taso tayi ihu amma mahaifiyarmu ta toshe bakinta saboda rok'on da mutumin kema babanmu akan muyi shiru Dan ALLAH, a razane matuk'a mutumin yake dan ko ina Na jikinsa mazari yake, yace a taimaka masa da ruwa yasha zaimana bayani, iya mahaifiyarmu ta nufi d'akunanmu dake cikin bargar dagacan gefe ta d'ebo masa ruwa a randa cikin kwanon sha ta kawo masa, babana ya taimaka masa ya fito daga akori kurar, ya zauna bisa buhun harawar da muka fara saukewa, ruwan ya kar6a ya kafa kai saida ya shanye kusan rabi sannan ya ajiye yana musu godiya, wani Abu irinna d'aukar hoto (camera) ya fiddo a cikin aljihunsa ya mik'ama mahaifina cikin yin magana da k'yar. yace____”. _“Sarkin Barga ga wannan abun, nasan zakayi mamakin miyasa Na bakashi, to banida wajen daya dace Na damk'ashi sai wajenka a kaf masarautarnan, Dan kaine hanyata mai sauk'i, akan wannan abun aka biyoni za'a kashe, shine ALLAH yabani ikon shiga motarku, dan nashigo tacikin kasuwa domin tsira da raina shine Na ganku, karka bama kowa camera d'innan sai d'an Sarki, Yarima Sameer, kokuma d'iyarsa, gimbiya Haneefa, ko matarsa uwargidansa wadda ta haifi su Yarima d'in, harda wad'annan takardunma, nasan ni tawa ta k'are Dan babu makawa saisun kasheni, Dan ALLAH ka tabbatar cikin mutane ukunnan ka bama wani, nasan yarima bashida wayon dazai fahimci minene, amma idan ka nuna masa yabama mahaifiyarsa zai bata, dukkan abinda ya faru da mai martaba yana acikin wannan Camera d'in, ni zan koma, Dan banason wani ya fahimci nama shigo masarautar nan balle har asan Na gana daku”._ “duk yanda mahaifana sukaso tsaida mutuminnan sun gaza, dan ya tabbatar mana dolene yabar masarautar a lokacin, saboda akwai munafukan da sukasan abinda yafaru da Mai martaba. Sai dai kuma abinda bamu saniba shine, Ashe dukkan abinda ya faru akan idon waziri ne, dan haka a wannan dare yabiyo sahun abinda mutumin yabada, mahaifana Na barci ya tashesu akan su bashi, sukace basusan mi zasu bashiba, shine ya kashe mahaifiyarmu wai dan baba yaji tsoro yabashi, dukda baba ya razana hakan baisa ya bashiba, ya yarda d'in gwamma a kasheshi shima da dai yabada , daga k'arshe shima ya kasheshi, k'arar da mahaifina yayi sai dukkan dokuna suma suka d'au haniniya. Hakanne ya sakani farkawa a rud'e Na fito daga d'akina, ina sako k'afata a d'akin mahaifana, Waziri Na cakama baba k'arfe a mak'oshi,, babana ya rik'e mak'ogwaronsa da hannu, yaringa min nuni da d'ayan hannun alamar Na gudu karnayi magana kuma, Na fahimci haka saboda ni baba yabama ajiyar abin d'aukar hoton da takardun, inhar iyayena zasu iya jurar mutuwa akan su bashi ni mezai hana na bi umarnin baba na gudu da abun, ko takan iyalaina banbiba na gudu ta hanya mafi sirri dana Sani, lokacin dana fito zan gudu waziri ya farga dani, hakanne ya sakashi biyo bayana, ganin bazai cinmini ba saiya saka dogarai masu tsaron k'ofa akan su bini wai na kashe iyayena zan gudu. Na rasa Inda zan dosa da wad'annan kaya saboda na tabbata ana bina a baya, saboda mun had'a ido da waziri, na shiga cikin jeji sosai, dan a wancan lokacin gari bai gama dunk'ulewa waje d'ayaba irin haka, Masarautar gagara badau ba tsakkiyar gari takeba kamar yanzu, dabarar hawa bishiyace tazomin dan haka na hau itaciyar wani Kalgo dake kusada k'oramar da mukan raka Yarima hutawa, har dogarannan da waziri ya saka su biyoni suka iso wajen domin nemana, ALLAH bai basu ikon ganinaba, saima suka wuce ni, lokacin sanyine sannan, nasha sanyi dan na wahala, sosai na fita hayyacina, abin mamaki da asubahi sainaji hayaniya a kusa dani, ido na bud'e da k'yar saboda tsantsar jigatar da nayi da muku-mukun sanyin wannan lokacin, wannan bawan ALLAHn nagani tare da Wanda yazo masarauta ya bamu abin d'aukar hoto (ya nuna baba Rabilu), hakanne ya sakani jin dad'i na sakko a nufin maida masa abinsa, nakuma sanar masa dalilin abin d'aukar hoton an kashemin iyayena, sai dai ina sakkowa wasu mutane na isowa wajen a mota guda biyu, yunk'urin guduwa mukayi mu duka ukun dukda su saima lokacin suka farga da ni a wajen, sun sami damar kama Wanda ya bama mahaifana abin d'aukar hoton, saboda kamar yaji ciwo a k'afa bazai iya guduwa ba, shine ya ringa fad'a mana mu gudu karmu sake mu basu abinnan. Iya k'arfinmu muka ringa gudu a lokacin Ranka ya dad'e, nashiga tashin hankali ganin rana tsaka masifa tazo ta haye mini ba tare dana san farkonta ba, gashi na rasa iyayena, na baro iyalina da k'anwata, bansan halin da suke cikiba, na samu damar shiga wani k'auye, Anan ne nasamu taimakon wani tsoho makaho, dan shine yabani mafaka ta tsawon shekaru 4, makahon tsohonnan yana zaune ne da matarsa amma ita tana gani, lokacin da jama'ar gari suka farga dani a gidan sai sukaje suka sanarma mai unguwar yankin, shikuma ya sanarma dagaci, har gida akazo aka tafi dani wani babban k'auyen dake kusa dasu inda dagacin yake akamin tambayoyi nida tsohonnan makaho, koda aka tambayi baba makaho saiya sanar musu ni d'an y'ar uwarsane, nazo ne na koyi sana'a na koma garinmu, dagaci yarigada ya yarda da baba makaho shiyyasa ya amince, aka kuma barni nacigaba da zama a k'auyen, tundaga wannan lokacin nasamu saken zama k'auyen gamji, ban sake waiwayar masarauta ba har tsawon shekaru hud'un nan. Saida ALLAH yayma baba makaho rasuwa sannan, matarsa gudun kar naci gadonsa shine tace yakamata na koma gida hakanan, ban mata musuba na had'o y'an kayana da abinda na samu a k'auyen da wad'annan takardu da abin d'aukar hoto nabaro k'auyen ina kuka saboda sabo. Sai dai abinda ban saniba Ashe anata bibiyata har lokacin, tun a hanyata ta shigowa gari wasu mutane suka farmin, na zubda komai nawa amma banda akwatin dana zubo abin d'aukar hoto d'innan da takarda, a cikin wannan gudu sai Ubangiji ya had'ani da wani bawan ALLAH akan besfa, ya bigeni, naji mummunan ciwo dan alamomin fitar rai sun bayyana agareni, cikin magana da k'yar, na mik'a masa akwatin ina rok'onsa dan ALLAH ya kar6i akwatinnan, ya Isar da shi masarauta amma yarima Sameer ko gimbiya Haneefa zai bamawa, ko mahaifiyarsu, bayansu karya bama kowa, idan bai samu damar badawa a yanzuba yabari sainan gaba inhar Yarima Sameer yay girman mallakar hankalinsa, zai iya kwatama kansa y'anci saiya bashi, na rok'esa karya ci amanata dan ALLAH, na aminta da shine shiyyasa na bashi....., da Sauri ya amsamin da insha ALLAH bazaici amanataba dan shima yana aikin jaridane, iya abinda naji kenan Daganan na suma a wajen, ban sake sanin komiba kuma, sai farkawa nai na ganni tare da wani maharbi jikinsa duk ciwuka, shine yaci gaba da kulawa dani tsawon lokacin ina jiyya, ban ta6a fad'amai ni waneneba, baikuma ta6a tambayata ba har shekaru sukaja, ganin girma ya kamashi sosai ya rok'eni na sanar masa daga ina na fito?, dan karya bar duniya da kokwanto a ransa, banyi nauyin bakiba na sanar masa komai. Yasha mamaki kwarai da gaske, dan suma labarin ciwon Sarki yaje musu, harma da nad'a k'aninsa da akayi ya maye gurbinsa. Shine yabani shawarar fara bibiyar masarauta kozan samu wani labari akan ahalina da jikin mai martaba, daga lokacinne nafara 6adda bamin shiga masarauta, na fahimci k'anwata ta auri wani bawa, matata ALLAH yamata rasuwa wajen haihuwar cikin dana barta dashi, d'an yayata data rasu itama ta bari shine k'anwata tacigaba da rik'o, a yanzu haka shine Wanda yazama direbanka Ranka ya dad'e, wannan shine abinda nasani ALLAH ya k'yautata rayuwarka, ya d'aukaki darajarka da mulkin masarautar gagara badau.” Daga Muftahu har Galadima ajiyar zuciya suka sauke, kowanne yana jinjina lamarin a zuciyarsa, shi dama baba Rabilu ya fad'a masa kafinsuzo, kafin Galadima ko Muftahu su sami damar magana baba Rabilu ya fara fad'in “Lallai kamar yanda na sanarmaka randa nazo gareka ranka yadad'e d'an uwanane shi wannan daya bada camera d'in, da ni da shi duk aikinmu d'ayane, bayan yakai wannan camera ga mahaifin Badi, gidana ya zarto, amma saiya iske ban dawoba sai iyalina kawai, yabar musu sak'on wasik'a da address d'in inda zan sameshi, wato k'oramar bakin gari inda shi Badi ya gammu, inayin sallar asubahi kuwa na nufi wannan wajen dan ya rubutamin Cewar yana cikin mawuyacin hali, yana tsaka da fad'amin abinda ke faruwa saiga wad'annan mugaye sun biyomu, bansan a ina sukaji muna canba, na gudu ne a tunanina shima Habu ya gudu, Ashe sun kamashi, saida na fara jiyo sautin muryarsa dake amsa kuwwar karmu tsaya mu gudu, badan nasoba na gudu nabar Habu a hannunsu, wasu a cikinsu sun cigaba da bina, amma wani mai lambu ya taimakeni ya 6oyeni, kwanana biyu a cikin lambun, saida mukaga komai ya d'an natsa sannan na fito Na koma gida, duk tunanina ai basu ganniba, shiyyasa nacigaba da y'an hidindimuna domin 6adda kama, a 6oye kuma na shiga binciken wanda Habu ya bama Camera d'in, dan ya gayamin tana masarauta wajen mai kula da barga, Labarin mutuwarsu tazomin shida matarsa a bisa bincikena, saidai a masarauta ance d'ansu Badi shine ya kashesu, Sam ban aminceba, wannan ya sakani Neman Badi domin na kar6i camera d'in hannunsa, inada tabbacin shine Habu ya sanarmin cewa gashi can alokacin da mutanen nan suka iso, saidai kallo d'aya namasa muka fara gudun tsira, daga nan kowa ya kama tsaginsa. Dole na ajiye aikina saboda tsaro, na kawo rigar siyasa na sanya dan nema ma kaina girma, shekarata 6 a rigar siyasa akayi yunk'urin kasheni, ba kowa bane da wannan aikin face Alhaji Shehu Adamu Darma, har gidana ya saka aka satoni, nayi mamakin ganinsa, dan jam'iyyarmu d'aya, wani sa6ani bai ta6a shiga tsakaninmu ba, dan haka na nemi dalilin sanin miyasa zaisa a d'akkoni cikin iyalina? bayan mu y'an jam'iyya d'ayane. Ya kwashe da dariya yana nunani da fad'in lallai Alhaji Rabilu fanisau bakada hankaki, a tunaninka dukkan 6addamin da zakayi bazamu ganoka ba? yanzu dai dukma ba wannanba, ina camera?. Nace wace camera kuma? Wani wawan duka yaronsa yamin, na dafe wajen saboda azaba, Darma yakuma cemin ina camera d'in da Habu idris ya bani? nanma na sanarmasa ban saniba, wannan ne yasakashi kar6ar k'arfe ya kwad'amin a kai saboda haushi, daga nan na fad'i a wajen, ashesu duk sun d'auka a lokacin dukna mutu, shiyyasa suka jefar dani gefen hanya suka tafi, wani bawan ALLAH ne ya d'aukeni yakai asibiti, abinda yasa su Darma basuji labarina ba wanann mutum ba d'an nan yankinmu baneba, fataucine ya kawoshi, daya d'aukeni kuma saiya bar nahiyar wannan yanki dani gaba d'aya, nayi jiyyar shekaru biyu, kafin na dawo dai-dai, duniya sukta d'auka na mutu, saida na d'au shekaru bakwai banzo wannan yankinba, dan bawan ALLAHn nan yazo har nan ya kwashe iyalaina ya kaimin, bayan yamusu bayanin dazasu fahimta, bayan shekaru bakwai nakanzo nad'anyi bincikena na koma cikin 6adda kamanni, a wannan yanayinne na farga da Badi, ban sanshiba gaskiya, amma ganin yanayinsa tamkar mai lek'en asiri shine na fara bibiyarsa harna fahimci wanene shi, hakama waziri da d'ansa, na lura kullum cikin bin diddigin yalla6ai Galadima suke suma, nima wannan abun shine abinda na sani, kunji dalilin Darma na kirana Fatalwa”. Galadima da Muftahu sunyi shiru cike da tsabagen rud'ani da al'ajabi, da k'yar Galadima ya iya bud'e baki cikin muryar tsananin damuwa yace, “waishin minene a cikin camera d'in nan? Yanzu kuma wanene ke rik'e da ita?”. Baba Rabilu yace, “Duk wannan muke son sani ranka ya dad'e, yanzu haka muna kan neman wanda badi yabama wannan Camera, dan na sanar masa har yanzu batazo gareka ba”. Galadima ya sauke ajiyar zuciya yana cije lips, idonsa yayi jazur, ya kalli Muftahu sannan ya kalli Badi dake zaune kansa a duk'e, “Badi yanzu idan ka gansa zaka iya ganesa kenan?”. “insha ALLAH ranka ya dad'e zan iya, saidai idan har ya mutune, bakuma ma fatan hakan”. Shiru dukansu sukayi kowa na nazari, Galadima sai ajiyar zuciya kawai yake saukewa, shi kad'ai yasan mi yakeji, ya kalli Muftahu yana fad'in “Sarkin mota ya shigo, dan nasan baisan matsayin Badi a wajensa ba”. Muftahu ya amsa da “to ranka ya dad'e”. Cikin y'an mintuna saiga Sarkin mota tare da Muftahu sun shigo, a k'asa ya durk'usa yana musu sannu, Galadima ya kallesa yana nuna masa Badi, “kasan wannan?”. Badi da Sarkin mota suka kalli juna, a lokacin ne Muftahu da Galadima sukaga kamannin su, saidai shi Badi tsufa ya 6oyesa kad'an. Ganin sun shagala da kallon juna kowa yakasa magana sai baba Rabilu ya katsesu da fad'in “Badi kamasa bayani mana”. Dattijo badi ya kamo hannun Sarkin mota kusa da shi, yana zubda hawaye yace, “matso gareni Yunusa, nine babanka yayan mahaifiyarka, Badi ya rungume Sarkin mota suka fashe da kuka, a haka yake bashi labarin alak'arsu. Saida kwalla ta cika idon Galadima, hakanne ya sakashi tashi ya fice daga falon, Muftahu da tausayinsu ya kamashi shima ya bi Galadima da hanzari. A tsaye ya iskeshi ya tsurama flowers d'in da akama gidan ado dasu ido, hannayensa biyu duk cikin aljihu, gaba d'aya bugun zuciyarsa ya fara canjawa, sai had'iye yawu yake da k'yar, wayarsa ya zaro daga aljihu, rasa wanda zai kira yayi, sai bin numbers d'in yake da idanu yana canki canka, ya tsansa dai ya sauka kan number Munaya......... ************************** Fitowata daga wankan yamma kenan Munubiya ta shiga, yau kwana biyu duk zuciyata babu dad'i, hakannan na tsinci kaina cikin 6acin rai, harzan fara shafa mai Aryaan ya shigo d'auke da Abdurrahman yana kuka, dole na ajiye man na kar6esa, na ta6a jikinsa da har yanzu zafin zazza6in daya yini da shi bai saukaba, saboda tunda asuba ya farka da kuka cibiyarsa na ciwo, kashinsa harya canja kala, saida innaro tazo tabashi magani sannan muka samu nutsuwa, daga nan kuma sai zazza6i, shine har yanzu nake d'an jin jikin nasa da zafi kad'an, nono na saka masa a baki kozai kama, dan duk yinin yau bai shaba, na sauke ajiyar zuciya ganin ya kar6a, ina shafa kansa idona na kallon fuskarsa data fara rikid'ewa zuwa kamannin mahaifinsa wayata ta shiga Ring, d'auke idona nayi daga kan Abdurrahman na maida ga wayar, nayi mamakin ganin yalla6ai, danna canja sunan tun a waccan ranar, na daiyi picking a d'arare na saka a kunne. yau dai banjira k'orafinsa ba nace, “Ina yini”. A yanda ya amsa min sallamar da gaisuwar saida gabana ya fad'i har na cire ma Abdurrahman nono ban saniba, aikam ya fashe da kuka. Hakkane yakuma rikita Galadima daga can, yace, “miya faru? Waye ke kuka?”. K'aramin tsaki naja, nace, “Abdurrahman ne, wai dama ka dawo?”. Bai amsa min na k'arshen ba saina farkon, yace, “mi'akai masa?”. “Babu komai, bayajin dad'ine kawai”. Lips d'insa ya cije yana fad'in “yanzu zanzo gidan”. Bai jira cewar Munaya ba ya yanke kiran. Sororo nayi ina kallon wayar, kai kace zan ganosa a wajen ne, Munubiya data fito ta katseni da fad'in “mikike kallo haka? ga ruwan nono kin bari yana zuba a jikin yaro”. Ajiyar zuciya na sauke, sannan na gyara ina kwantar da Abdurrahman d'in dayay shiru. Munubiya dai takuma tambayata, fad'a mata zuwan Galadima nayi, tace, “oh shine kikema wannan mamakin ko miye?”. 'Dan hararta nayi, amma bance komaiba, itama ta ta6e baki tana kamo hannuna ta zauna a stool d'in Mirror. Wai sai tamin kwalliya. Da faro k'in yarda nayi, saida naga ta 6ata rai sannan na hak'ura dai tamin inata tura baki gaba.....................✍🏻 *_ALLAH Sarki, wlhy harna fara missing d'inku, waya tamana tsiya😢, yanzuma da wayar Oga nayi typing, koba komai Comments naku na sakani nishad'i, I Miss you so much all😔😘😘😘❤❤_* Insha ALLAH vary soon zan dawo gareku😂. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻_* *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣1⃣➖1⃣2⃣ .............Mintuna basufi 20 da gama kwalliyar ba saigasu Aiyaan sun shigo dad'an gudunsu, Munaya na cikin d'aki tak'i fitowa, wai kunyar su inna suganta da kwalliya takeyi. Inna ta dakama su Aryaan tsawa saboda batason wannan gudun. Nutsuwa duk sukayi. Tace, “Gudun mi kukeyine?”. Y'ar rige-rigen fad'a suka fara, kowa yana ture d'an uwansa akan shine zai fara fad'a, ana cikin haka Yaa Anas yay sallama. Hayaniyar su Aiyaan ta hana aji, sai laraba ce ta farga dashi, shine Yakuma yimasu Aiyaan tsawa suka nutsu, kowa ya zauna gefe yana tura baki. Yaa Anas ya gaishe da laraba da innarsu munaya, Munubiya ma ta gaisheshi, ya Amshi Ameen dake hannun inna yana fad'in “inna Yalla6ai Galadima ne fa agidan namu, gashi kuma duk su Abba basa nan, shine nace ko'a kawoshi nan ne”. Inna tace, “A'a Anas, ai ba'ayi hakaba, bara na d'akko makullin d'akin Abbanku saika bud'e masa nan ya shiga”. Anas yace, “to inna”. Laraba dake taya Munubiya shirya su Amaturrahman tayi murmushi, a ranta tana yaba yawan karamci na ahalin Munaya, mutanene masu dattako da sanin darajar d'an Adam, shiyyasa kullum take kuma taya Galadima murna da samun tsatson wannan mutane....... Tunaninta ya katse lokacin da inna tadawo da key ta bama Anas, Ameen ta kar6a a hannunsa shikuma ya fice. Munubiya tace, “innarmu ajiye wannan ki k'arasa sama Abdurraheem kayan Dan ALLAH, sainaje na had'ama Abbansu abincin, nasan yanzu yayi”. Inna ta harareta, “kai nifa kunma maidani Nanny d'inku, nizan ke muku hidimar y'ay'ane?”. “please mana innarmu, basune masu kawo miki kaza kina ciba sannan kin tsufa”. Laraba tayi dariya tana fad'in “Gaskiyarki kuwa Maman 2, ALLAH dai yaja da rai”. Inna tace, “iya kema biyema shirmennan nata zakiyi?”. Laraba takuma darawa tanama Abbdurrahman rawa. Itadai Munubiya ta fice tabarsu, laraba na bama inna amsa. Duk ina jiyosu daga d'aki, haka kawai sainakejin wani iri, yanzu dole ta gaban su Innarmu zanbi natafi wajensa? Na kalli kaina a mirror kunya ta kuma kamani, dukda Simple kwalliya Munubiya tamin nayi k'yau, dan d'aurin kaina ya zauna dak'yau, fuskata ta kuma nutsuwa, har rantsuwa tamin inhar na canja wani Abu saitayi 2weeks batamin maganaba, nasan kad'an kenan daga abinda Munu... Zata iya, shiyyasa dole na hak'ura na bari..... Shigowar Munubiya yasani waigawa na kalleta, ta harareni tana matsowa tamin kallon tsaf, nasan sotake taga mina goge kona canja, ganin komai yana yanda tayishi saita kuma d'aukar soson hoda ta gyara, ta d'akko turare tana kuma fesamin, hannunta nai saurin rik'ewa ina 6ata fuska, “Wai Sweetheart bazaki barshi haka bane? Turaren nan har hawa kaifa yake, Ni wlhy kunyarma fita nakeyi”. Munubiya ta fisge hannunta tana dariya da fad'in “to kibi ta k'ark'ashin k'asa kawai mana, kuma wlhy ki nutsu, idan yauma tsiwar zaki masa saiki bada himma, anacewa mutum Idan ya haihu yana hankali kedai bakiyiba, saima rashinsa kika k'aro, malama muje yana jiranki”. Yanda kukasan na make Munubiya haka naji, amma saina k'yaleta, nima nasan ta hanyar da zanbi na rama, gyalen data samin a kafad'a nabi da kallo. nace, “haba Munu, amma wannan d'an gyalen Dan ALLAH?”. “Okay, wajen surukinki zakine? ALLAH ki kiyayeni”. Baki na murgud'a mata. Tace, “oho dai, kije kimasa kidawo ta cinyayyen lips, danba barinki zaiyiba”. Juyawa nayi na kalleta, amma saita d'auke kai tamkar bama itace tayi maganarba. Nayi kwafa kawai muka fito. ALLAH ya soni babu kowa a falo sai su Aiyaan, hakkane ya sakani sauke ajiyar zuciya nad'an saki jikina. Gwaggon Haleematu dake kaikawo a kitchen da tsakar gida saboda itace ta kar6i girki tabimu da kallo, gulma nacin ranta, daga ni har Munubiya d'auke kai mukayi tamkar bamu gantaba, muka shige falon Abba da takalman Galadima heif cover milk ke a k'ofar. K'amshin turarensa yafara amsa mana sallama, na shak'a na lumshe ido. Hankalinsa nakan yaransa da duk suke jikinsa, yana sanye cikin milk d'in shadda harda hular zanna bukar itama milk da d'an kwalliyar Brown kad'an, sosai yamin k'yau amma saina d'auke kai tamkar banma gansa ba. Munubiya tace, “To Abban 3 gatanan nakawo maka”. Murmushi yayi, idonsa sanye cikin farin eyeglasses, cikin muryarnan tasa mai kama da anmasa dole yace, “Thanks you Auntynmu”. Murmushi itama Munubiya tayi, ta jinjina masa kai ta juya zata fita, har takai k'ofa ya katseta da fad'in “Su twins rowarsu akemin?”. Hannu ta saka ta dafe bakinta, saikuma ta janye tana cewa, “A'a Abban 3 zasuzo su gaida abbansu insha ALLAH”. Baice komaiba sai murmushi daya sakeyi. Ta harareni sannan ta fice, Nina ramawa nayi. Koda Munubiya ta fice saiya kuma maida hankalinsa ga yaran ya shareni, abin yabani haushi, jinaima kamar na fice abina, amma na danne zuciyata na matsa gabansa. Wajen tiren abincin na durk'usa, na d'auki jug d'in zo6on na zuba a k'aramin cup, d'agowar da zanyi na kamashi yana kallona, amma saiya basar, baki na tura kad'an, na mik'a masa cup d'in. Bai kar6aba, sai wani bina da kallo yake tundaga sama har k'asa, a raina nace rainin wayo. Idonsa ya janye daga kaina, ya fara kwantar da yaran d'ai-d'ai a gefensa, saboda a doguwan kujera yake. Saida ya gama nakuma mik'a masa cup d'in, hannuna ya had'a da kofin ya rik'e, na d'ago ido muka kalli juna, duksai na daburce, danya cire eyeglasses d'in, kamar mai koyan magana na had'o kalmomin gaisuwar da gyar. Nace, “i...na..yini”. Wani Munafukin murmushi yayi yana lumshe idanu, ya kuma bud'esu a kaina yana d'age girarsa d'aya da cizar lips, a hankali ya furta “ke matsoraciya Ce, miye na rikitar daga kallo uhmyim?”. Idanuna nad'an juya nace, “Tab badai niba”. Ya ta6e baki kad'an, idonsa akan hannunmu dake had'e waje d'aya akan kofin. Nima saina kalli hannun, cikin sanyin muryar dabansan nayiba nace, “da sanyi fa”. “Really?”. Shiru nayi ban amsashiba, ya zame kofin a hankali, sannan ya koma jikin kujerar ya kwanta yana hard'e k'afafu. 6oyayyar ajiyar zuciya na sauke, bansan miyasa inhar Galadima zai kasance kusa dani daf irin haka koya kafeni da ido nake rikicewa ba, haka kawai sainaji jikina yana tsuma... Yay wani luuu da idanu saboda ajiyar zuciyar da tayi, zo6on ya kai bakinsa ya kur6a kad'an, dad'insa ya sakashi lumshe idanu ya had'iye. Da hannu yamin nuni da kujera, tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki na mik'e, harzan bar wajen naje ta nesa dashi saiya rik'o hannuna. Juyawa nai na kallesa, ya nunamin kujerar kusa dashi da ido cikin tsare gida. Banida za6in daya wuce bin umarninsa, na zauna tamkar mai shirin guduwa da ance ar. Zo6on yakuma sha yana kallona, kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru. Ganin haka sai nace, “yaya jikin Abie? dasu Momma?”. Yaji dad'in ganin ta damu da ahalinsa, ya ajiye kofin yana gyara zama, yace, “jikin Abie Alhmdllh munata k'ara ganin haske, duk since na gaidaki dak'yau”. Nace, “ina amsawa”. Daganan mukai shiru, kowa yana tattaunawa da zuciyarsa, Idan ka gammu saika d'auka wasu saurayi da budurwane, irin had'uwar farko d'innan😂. Abimda na fahimta dai kamar yana tattare da damuwa ma, nad'an kallesa ta gefen ido, idonsa nakan yaransa, nace, “Abinci fa?”. Maido da kallonsa yay gareni, yad'an yamutsa fuska yana girgiza kai. Kallonsa nayi, cikin marairaicewar da bansan nayiba nace, “please mana yalla6ai, yanzu haka bakaci komaiba ka fito gida”. Wani Abu dabaisan miyeba yaji ya tsarga cikin kansa har zuwa tafin k'afa, idonsa k'yam akan Munaya ko k'yaftawa bayayi, itama gareta hakanne, ta zuba masa ido batare da ta shirya hakanba, sai tsantsar tausayinsa dayake hangowa cikin idanunta, hannunta ya kamo cikin nasa, yana fad'in “kinaso naci?”. A sanyaye na jinjina masa kai alamar eh. Murmushin gefen baki yayi, ya matsa hannunta kad'an, “indai kinason naci akwai sharad'i”. Batareda nasan mi bakina ya fad'aba nace, “kafad'a kona miye na amince”. Kansa ya jinjina yana janye hannunsa, ya gyara zamansa yana fuskantata sosai, akan la66a ya furta, “saidai idan zaki bani da kanki”. Babu shiri na waro manyan idanuna ina dafe baki alamar mamaki, ya had'e fuska yana ta6e baki da kwantar da kansa jikin kujerar. Yace, “Ashe ba sokike nacinba, kuma yunwa nakeji”. Harga ALLAH inason yaci, dan na fahimci yanada buk'atar abincin, amma yana azabtar da kansa saboda bai yarda yaci na kowaba amasarautarsu, idan kuma ya fito inhar ba birnin gayu yajeba bazai ta6a cin komaiba inba ruwa ba harya koma gida kuwa... Na sauke ajiyar zuciya, idona cikeda kwalla nace “to amma...” Idonsa ya bud'e ya d'agamin hannu, amma baice komaiba. Nima ban sake yunk'urin cewa wani abunba, na sakko daga kujerar na durk'usa a k'asa ina bud'e kulolin. Mamaki ya kamani, dan ganin masa, a ina Munubiya ta samo masa haka? A lokacin da tasan zaizo yayi k'arancin da har za'ayi Masa. ganin babu mai amsamin tambayar na zuba hud'u a plate d'in, na d'ago ido na kallesa, Ashe shima ni yake kallo, idanu ya lumshe alamun ya Isa. Nima saina jinjina kai, kwanon da zansa miya na d'akko, amma saiya rik'e hannuna yana girgiza kai, na kalli plate d'in masar sannan na d'ago Na kallesa, ya kad'amin kai. Fahimtar mi yake nufi da nayi saina zuba miyar gefen masar, sannan na mik'e da nufin komawa inda na taso, tiren abincin ya janye gefe, ya jawo center teble d'in a gabansa sosai. Kallon teble d'in nayi shima na kallesa, saiya d'auke idonsa, a yanda ya janyo teble d'in inhar na zauna dolene k'afafunmu suke gogar juna, amma ya zanyi tunda na d'auki alk'awari. Zama nayi, na d'ora plate d'in saman cinyata, na d'ebo masar da spoon na nufi bakinsa, baki ya ta6e yana girgiza kai. Na dafe kaina irin naga ta kaina d'innan, na kallesa a marairaice, “yalla6ai to ya kakeso nayi please?, kaifa kace zakaci”. Da d'an yatsa ya nuna hannuna. Cikin mamaki nace, “da hannu?”. Yanda tai maganar tana zaro ido saiya so bashi dariya, amma ya had'iye kayarsa. “O ni Munaya naga ta kaina”. Nafad'a a hankali. A ransa yace zadai ki gani yarinya. Dole na mik'e nakuma wanko hannuna a bayin falon Abba, na dawo, gyalena na zame dole na shinfid'a masa saman cinya gudun karna 6ata masa kaya, na fara d'ibar masar kamar yanda yake buk'ata na nufi bakinsa, saida ya kama hannuna sannan ya k'arasa dashi cikin bakin, ALLAH sai da tsigar jikina ta tashi, amma na daure nakuma d'ibowa, haka naita bashi har ya cinye, na bashi nama ya girgiza kai, alama namasa a k'ara?. Da d'an yatsa ya nunamin wai d'aya, bud'e kular nayi na d'auka, sauran miyar plate d'in ta isa, zan gutsura ya rik'e hannuna, a mamakina sainaga ya d'an ja hannun rigarsa sama ya saka hannu a plate d'in, idanu na waro da bud'e baki Dan mamaki, sai kawai naji hannunsa cikin bakina ya sakamin masa, ya d'agamin gira d'aya damin alamar inci, tamkar sokuwa haka na shiga taunawa, harna had'iye idonsa nakan bakina, saida ya rage saura lauma d'aya ya dakata da bani, na ida d'aukar laumar k'arshen na saka masa nima, ina niyyar tashi na wanke hannu ya maidani zaune, hannun dana bashi ya kamo yana sud'ewa, salon dayake lashe miyar saiya haifarmin da kasala, na rumtse idona harya gama sannan ya sakarmin hannu. Nima saina kama nasan na tsotse sannan na mik'e, ina toilet zan wanke hannuna zan d'ibo shima nakawo ya wanke sai na jishi a bayana, juyowa nayi na kallesa, ya mik'amin hannunsa. Bance komaiba na kama na wanke masa, na zuba masa ruwa ya kuskure bakinsa. Nidai gaba d'aya mamaki dukya nemi halakani. Koda muka fito ina niyyar komawa inda na fara zama sai naji an fisgoni, jikinsa na fad'a, bance komaiba dukda naji zafi. Shima baice uffanba. Lallai akwai abinda ke damunsa da gaske, hannuna na d'ora a kan k'irjinsa saitin zuciyarsa, ya bud'e ido sosai yana kallon hannun nawa, cikin aro jarumta nace, “Autan Momma mike damunka wai?”. Murmushin dabai shiryaba ya saki, ya kalleni ido cikin ido yana fad'in, “kin rainani ALLAH kuwa, wannan autan bazai bar bakinkiba dai ko?”. Murmushi nayi mai sauti, har hak'orana na bayyana, na had'e hannayena a waje d'aya alamar ban hak'uri, cikin langa6e kai nace, “tuba nake to na tsakkiya nefa kai ashe”. Rankwashi yamin a kai, na dafe wajen dukda d'ankwali yasa banji zafiba sosai, amma na 6ata fuska ina k'ak'alo hawayen k'arya. Gira d'aya ya d'age yana kallona alamar yadai?. Na tura baki gaba ina fad'in, “da zafifa”. Murmushi yayi yana kauda idonsa yana kallon yaransa. Na yunk'ura da nufin sauka a jikina amma ya rik'eni, ba tare da ya kalleniba yace, “yakamata kisan kin girma”. Bakin na kuma tunzurawa nace, “hu'im ina nan a babyna wlhy”. Shi kansa baisan k'aramar dariya ta kufce masaba, ya d'an dara yana girgiza kai da kallona. Ganin ya fara sakin jikinsa saina kuma cewa “Please yalla6ai bakada lafiya ne?”. Tafin Hannunsa ya sanya saman kumatuna, a hankali tamkar mai rad'a yace, “mikika gani?”. Na d'an kuma kwantar da murya ina janye idona daga cikin nasa, “Ba komai, kawai yanayinka ne ya nuna”. Baice komaiba ya matso da fuskarsa gab da tawa ya had'e bakinmu, dukda na tsorata kar wani ya shigo ya gammu haka na barsa, yayi yanda yake so inhar hakan zai kauda damuwar dake ransa, nidai fatana na cika alk'awarin dana d'aukarma Momma a duk sanda na gansa cikin damuwa. Saida ya gaji da kansa sannan ya bari tareda rungumeni yana sauke ajiyar zuciya, muryarsa can k'asan mak'oshi yace, “haka kike son ganina”. Kaina na girgiza masa, ya d'agoni da sauri yana kallona, yace, “to yaya?”. Murmushi nayi nafad'a k'irjinsa ina 6oye fuskata saboda kunya, shima saiya saka hannuwansa ya zagayeni yana murmushin, a hakanla ya furta “Thanks”. Bance komaiba, amma naji dad'i daya godemin. Kiran wayarsa da akayi ya sakani tashi daga jikinsa, zan tashi gaba d'aya ya rik'eni, a haka yay picking call d'in, na fahimci da papi yake waya, dukda kakansa ne yanda yake magana cikeda tsantsar girmamawa saiya birgeni, *_Mai dawakai_* danaji yana ambata da bayanin d'ansa mai suna Badi ne yaja hankali na, tsaf na fahinci zancen dukda bansan mafariba, yakuma yanke maganar bai k'arasaba yana fad'ama papi sai yazo zasu k'arasa zancen. Yanke wayar yayi yana huremin ido saboda kallonsa dana keyi, tunda ya fara wayar. K'asa nayi da kaina dan naji kunya ya kamani ina kallonsa, ya ajiye wayar yana fad'in “Zamukai Abdurrahman asibiti ne?”. Kaina na girgiza masa. nace, “A'a aiya warke bama sai an kaisa ba”. Yace, “Okay”. Idonsa akan yaran, Abdurraheem ya fara motse-motsen tashi, sauka nayi a jikinsa nakoma gaban kujerar na durk'usa ina d'an bubbuga bayansa, dan banason ya tashi, inhar ya tashi saiyasha nono, sauran kuma suma duk tashi zasuyi, bada nono a gaban Galadima shine abinda nake gudu ni kuma. Shikam tsura musu ido yayi cikeda sha'awa daga ita har yaran, ya d'auki wayarsa yamusu hoto batare da ta saniba. Saida naga ya koma barci sannan Na dawo kujerar dana fara zama, shima zamansa yagyara yana kallona, magana yakeson yi amma yanata juyata a zuciya, nidai bance dashi komaiba, saida ya gama k'asaitarsa da basarwa sannan yace, “Abba fa?”. Nace, “yayi tafiya yau kwana biyu”. “zuwa ina kenan?”. “wlhy ban saniba, amma miya faru?”. Kansa ya girgizamin alamar babu komai, yad'an furzar da huci yana kallona agogon hannunsa. “Shikenan ni zan wuce, zan iya dawowa a kowane lokaci inhar Abba ya dawo”. Kaina na jinjina masa, ya mik'e, nima saina mik'e ina fad'in “yaa Sauban fa?”. Bai tankaminba saida ya duk'a yayma yaransa kisses a kumatu sannan ya d'an kalleni ya d'auke kansa, “Tare muka dawo, amma zai wuce masarautar su papi gobe, dan a can zai zauna harya gama”. “ALLAH ya bada nasara”. Nafad'a ina sauke ajiyar zuciya. A kan la66a ya amsa da amin. Harya kusa nufar k'ofa nace, “bakace komai game da maganarmu bafa”. Cak ya tsaya amma bai juyoba, a haka yace “wace magar?”. Wani yawu na had'iye da k'yar ina fad'in, “Maganar rabuwa, nifa gaskiya bazan komaba”. Saida yaja kusan seconds 20 kafin ya juyo yana fuskantata, kallon da yakemin yasani janye idona daga kallonsa, cikeda k'asaitarsa yatako ya dawo inda nake tsaye, hannayensa ya cusa cikin aljihu yay matuk'ar d'aure fuska, cikin izzarsa yace, “wai nikam miyasa kikeda naci?”. Nima fuskar na tamke. Nace, “Neman y'ancina nake, tun farko a wannan tubalin ka gina auren, mizaisa kuma lokacin rugujeshi yayi bazakayi hakanba?”. Lips d'insa ya ciza yana kallona da k'ank'ance idanu, cikin salon Basarwar tasa yace, “So what idan nine na gina a haka d'in? Kinsan dai bazaki ajiyemin yara ba koda abinda kikeson ya kasance, dan yarana bazasu sha madaraba bayan sunada abinci”. “Humm” na fad'a cikin takaici. na gyara tsayuwa idona na cikowa da kwalla, “Yalla6ai karka manta a randa na kwana biyu gidanka da bakiknka ka tabbatar min baka zalunci? daga ni har kai mun amince cikin yarannan ya zone cikin k'addarar dabamu shiryama zuwanta ba, to mizaisa kuma zuwansu duniya yazama salon tauye hak'k'ina? Na amintane da aurenka domin warware k'ullun da akaimin da wanda yake kan mahaifina, bawai dan bansan y'ancin kainaba ko darajata, idan har nice a matsayin Amaturrahman zakaso wani ya aureni a matsayin auren shekara d'aya ko biyu domin cikar wani burinsa ya rabu dani?, addininmu da al'adarmu duk basu koyar damu hakaba, anayin aurene domin ibada, saboda bautar ALLAH ne, sannan ana ginashine bisa tausayi da rahama, inhar zuciyarka bazatayi dad'iba a matsayinka na mahaifin Amaturrahman idan hakan ace akanta ta kasance, to ya kake tunanin randa nawa mahaifin yasan gaskiyar matsayin nawa auren zaiji?, tunda nataso nake d'and'anar zafi da d'aci na zamantakewar rayuwar gidan yawa, taya zanso saka rayuwata a walagigin kila wa kala, na shigo wannan yak'inne domin neman y'ancin kai badan ribantuwa da ganima ba, amma lokacin dana wayi gari da abinda ban shiryamawa ba a cikin jikina haka na hak'ura na kar6a da hannu biyu saboda k'ok'arin cinye jarabawa, miyasa kakeson yin wasa da rayuwatane wai? Duk motsi dai yaranka! Yaranka! Karka manta nimafa y'ar wasuce, kamar yanda kakeji haka suma sukeji akaina, inason nima nayi aure na zauna tamkar kowacce mace a gidan mijinta, na fidda hak'insa da ALLAH ya wajabta min, shima ya fidda min nawa da ALLAH ya wajabta masa......”. Hannu ya d'agamin alamar ya isheshi haka, yakuma matsowa gabana cikeda izza yace, “mikikeso yanzun?”. Nace, “sanin matsayin aurena, inhar yaranka ne zan muku sadakar shayarwa na wata shida na yayesu nayi aurena da mijin dazai soni ya k'aunaceni domin ALLAH”. Bakinsa ya ta6e yana cije lips, jijiyoyin kansa duksun mimmk'e saboda 6acin rai, cikin takaici yace, “Yarinya har abada babu shegen namijin daya Isa na k'etara gona shima ya k'etarata, koda kuwa wannan gonar ta jinginace, ko ayanzu nabar duniya wani yayi hakan ban yafeba, duk gonar dana ra6a tawace ni kad'ai koda banyi noma a cikinta ba, wannan yazama first and last da zaki kuma kawomin irin wannan maganar, kodan kinga ina k'yaleki ne shiyyasa kike d'aukata wani sauna kiringa min zancen wani banza can daban, Munaya karki yarda na nuna miki a salin true color d'ina wlhy, ina kuma gargad'arki a karo na k'arshe”. ‘ya k'are maganar da bugamin yatsunsa biyu saitin fuska ya fice abinsa’. Baki na ta6e ina bin inda yabi da harara, sannan na saka gyalena na goge hawayen dake zarya a kumatuna nai kwafa na fice abina nima nabar yaran. ************************** Tunda ya fito Muftahu ke binsa da kallo, harya bud'e mota ya shiga baiko kalli Muftahun ba shi. Dama shine ya kawoshi, amma yana ajiyeshi ya koma saboda wani aiki daya bashi, dawowarsa kenan yana k'ok'arin kiransa yace zai shigo su gaisa da Munaya shine yafito a fusace. Baice dashi uffanba ya bud'e motar shima ya shiga ya tada suka tafi, saida sukayi nisa da tafiya sannan Muftahu yace, “Ranka ya dad'e wai mike faruwane?”. Shiru yamasa yak'i tankawa, shima Muftahu sai yaja bakinsa ya kulle ya cigaba tuk'insa. Sai jera tagwayen tsaki yakeyi, Muftahu ya kuma kallonsa sannan ya maida hankali ga tuk'insa, ya kuma rik'e sitiyarin yana fad'in “ALLAH ya huci zuciyarka ranka ya dad'e, idan kana ganin bazaka juri zuwanba kace ta dawo mana kawai”. Cikin jan wani tsakin yace, “inhar taci gaba damin zancen wani wawa lallai zan datse harshenta wataran”. 6oyayyan murmushi Muftahu yayi, a zuciyarsa yana jero hamdala wa ubangiji, dan babu abinda yake hange tattare da galadima sai tsantsar kishin matarsa, dukda baisan miya had'asuba yaji dad'in hakan, koba komai yanzu ya fita daga damuwa da fargabar rabuwar wannan auren. cikin son kuma fahimtar wani Abu yace, “to amma ranka ya dad'e yazamuyi idan lokacin rabuwarku yayi kenan? Kasanfa alk'awarin da mukai mata”. “Oho! Maka”. Galadima ya fad'a cikin tsananin fusata. Da k'yar Muftahu ya iya had'iye dariyarsa, bai sake cewa komaiba har suka isa gidan baffi, dan karya mazgeshi a banza. Muftahu ya fita domin nema masa ison shiga ciki, a lokacinne yasamu yay dariyarsa mai isarsa, lallai Galadima akwai kishi, tashin hankali, irin wannan ajiyar zuciya haka. *************************** Tunda na shiga Munubiya take bina da kallo, ta ce, “ina yaran?”. “Suna can”. ‘nafad'a ina shigewata ciki’. K'ala bata sake cewaba tafita abinta. Har dare ina fushi, nak'i kula kowa, innarmu yitai kamarma batasan inayiba, dukda batasan mike damunaba, Munubiya ma shareni tayi, sai laraba Ce ke tambayata kodai banajin dad'ine?, nace a'a. __________________________ Saida Muftahu ya raka Galadima har falon Baffi sannan yace zaije ya dawo kafin su gama. kansa kawai ya d'aga masa amma bai tankaba. Fitar Muftahu babu dad'ewa baffi ya fito shima, zama yay idonsa akan Galadima, dan ganinsa cikin damuwa, “d'an baffi miya farune haka?”. Galadima yafara k'ok'arin saita kansa cikin k'ak'aro murmushi yace, “Babu komai Baffi”. Duk da bai gamsu ba saiya k'yaleshi, dan maybe ba huruminsa baneba, yace “Alhaji Rabilu yakai maka bak'o ko?”. “Eh d'azunnan muka rabu dasu, abindama ya kawoni kenan, dan ina ganin insha ALLAH mun sami dukkan bakin zaren, zan fara aikina kawai”. Murmushi baffi yayi yana gyara zamansa, yace, “eh to ansami bakin zare kuma ba'a samuba, dan yanzu binciko Wanda Camera d'in take hannunsa shine babban aikin dake gabanmu, dan itace babbar hujjarmu bayan d'unbin hujjoji da muke dasu a k'asa”. Galadima ya sauke ajiyar zuciya yana jinjina kai, “hakane Baffi, amma akwai dai wasu y'an bayanai danake dasu a hannu yanzu haka, sai dai banida tabbacin dai-dai ne? Kokuwa akasin haka, amma kama SD da mukayi shine zai fito da gaskiyar hasashen nawa”. “To shikenan, ALLAH yasa muji alkairi”. “Amin, saidai ni a bayanin Baba Rabilu akwai abinda har yanzu yakemin rawa a zuciya”. “tofa, minene kenan?”. “Maganar siyasa dayacemin ya shiga a wancan shekarun, bayan kuma lokacin mulkin sojane, kenan wace siyasa sukayi?”. Baffi yay murmushi, “wato abinda na fuskanta anan shine, yasako kalmar siyasa ne domin mu mufasa sauran bak'in da kanmu, amma tabbas a wancan lokacin babu wata jam'iyyar siyasa, wayema ya Isa d'aga murya akan mulkine? Saidai bincikena ya nuna Dalilin kafa Group nasu tanderu yanada nasaba da son kafa mulkin farar hula, wato sunason mulki yabar hannun sojoji kenan, saidai a 6oye sukeyin dukkan abinsu, har suka ringa jawo ra'ayin mutane mabanbanta a cikin tafiyar tasu, abinda na kasa fahimta nima shine, shin sunjawo Alhaji Rabilu ne dansu tabbatar Camera na hannunsa? Kokuwa shine yakai kansa garesu domin lek'en asiri? Dole cikin biyunnan a samu d'aya, kodan yunk'urin kasheshi da suka saka Darma yayi”. Galadima dayay shiru yana fassara zancen Baffi dak'i-daki ya shiga jinjina kansa alamar gamsuwa da bayaninsa, zuwa can yace, “Baffi ka bani kwanaki biyu zanyi bincike insha ALLAH, dan zan tattauna da SD da kuma Harun, sannan akwai yaron da aka saka yay aikin da aka buga a jaridarnan, shima inason yazo hannuna insha ALLAH ”. “ALLAH ya cigaba da dafa maka, Yakuma tsareka da dukkan sharri, lallai ka ringa kulawa, dan yanzu dukkan wata hanya da zasubi domin cuta maka sun tanadeta, karka d'auka suma basa bibiyar lamarinka kamar yanda kake bibiyar nasu, dan ranar naga Alhaji Abdul- Naseer da wani masanin Computer, saidai shi bai ganniba, nasha jinin jikina kwarai da gaske, amma nikam inamason tambayarka, minene alak'ar Surukinka da senator halluru ne?”. “kamar dai abokinsa ne baffi”. “Ok! Ok! To lallai ka sanar masa ya lura, dan Senator Halluru yaronsu tanderune, za'a iya bi ta hanyar surukinka a 6ata mana aiki, tunda sun san akwai alak'a tsakanin kai da shi”. “wannan gaskiyane Baffi”. Sun cigaba da tattaunawa akan matsalolin da ayanzu zasu fuskanta, baffi na kuma bama Galadima dabaru a shara'ance Wanda bazai aikata abinda shima zai rufta ba. Sai dare ya koma masarauta, yinin yau gaba d'aya a tsaye yayisa, shiyyasa duk jikinsa ciwo yake masa, yanayin zirga-zirga amma ba irin wannanba mai cikeda cajin kwakwalwa da rikitar tunani. Ga maganganun Munaya dake cin ransa, ya tabbata duk gaskiya ta fad'a, hakan datake yana kuma tabbatar masa da tasan darajar kanta, inda watace shiru zatayi sai yanda yaso yi da ita, duk kuma abinda zai mata koda Mara k'yaune zata shanye saboda kasancewarsa d'an wani, amma duk da kasantuwarta mace kuma wadda take k'ark'ashin mulkinsu ALLAH bai sakama zuciyarta tsoro ko kwad'ayi ba, itadai kullum burinta shine asan darajarta da kimar ahalinta, sa6anin y'an matan yanzu da duniyar Ce kawai burinsu da son ganinta a tafin hannunsu, auren mai kud'i ko mulki, mai k'yau ajin farko, na nunama k'awaye da yin alfahari a duniya, yasan darajarta kona iyayenta wannan ba matsalarta bace, yanada addini ko kula da addinin shiyya Sani, son gaskiya yake mata ko albarkatun jikinta yakeso batada matsala, ya zube a kujera yana sauke tagwayen numfashi. Sauban dake zaune yana kallo yakuma kallonsa, yayansu na bashi tausayi, saidai shi taurinkai da rashin yarda da kowansa ke had'ashi dashi, amma ta wani fannin yakan kalli hakan a matsayin gaskiyarsa, dan massarautar tasuce abar tsoro, ba kowane abin yardaba, yanda zaka tantance na kirkin shine mai wahalar kuma. ********************* Na kasa hak'uri da danne maganganun Galadima, hakanne ya sakani yanke shawarar tambayar Munubiya kota Sani, saida mukai shirin barci dukda sharenin da takeyi nadai danne nawa Fushin na zauna kusa da ita tana shayar da Meenat data tashi. Kan yarinyar na shafa sannan nace “Munubiya in tambayeki mana please?”. Kamar bazata kulaniba sai kuma ta kalleni. Tace, “Ina saurarenki”. Ajiyar zuciya nayi ina gyara zamana, nace, “dan ALLAH idan namiji yace gonarsa mi yake nufi?”. Jimm tayi alamar tunani, ta kwantar da meenat tana fad'in “Matarsa”. Da mamaki na kalleta, yayinda wani sanyi ya ratsa raina, amma na danne....... Ta katseni da fad'in “Munaya ki fito fili ki sanarmin abinda ke faruwa, kinsan banason kwana-kwana, sirrinki keda mijinkine kawai a rayuwa bazanso saniba, domin ALLAH ya haramta bud'e wannan, saikuma yankin sirrinsa na rayuwa Wanda yarda da matarsane kawai zaisa ya fad'a mata, shima wannan kirik'e masashi, amma Munaya na fuskanci har yanzu babu dai-daito tsakaninki da mijinki, duk da kin sanarmin da manufar aurenku nazata darajar zuri'ar data shigo tsakkiyarku zai kawo muku sasanci Ku manta da wani auren Contract, duk da na fahimci mijinki jinin mulki na yawo a jikinsa, danne Abu a rai da basar dashi tamkar jinin jikinsa yake, kekam nasan halinki mutumce maison a damu da ita, sannan a nuna mata komai a aikace da furucin baki, kema danaki jinkan Wanda bansan gidan uwarwa kika samoshiba, amma mike wakana a duniyar aurenki? Mikuma kuke shiryawa keda surukarki?”. Shiru nayi nakasa magana, dan banso fitar da wannan sirrinba har zuwa lokacin da Momma ta bani, duk da nima rashin sanarma y'ar uwata yana damuna, dan bamu ta6a 6oyema juna wani abuba, ko akan aurena daga baya kasa daurewa nayi na sanarmata, duk da na 6oye matanne saboda gargad'in da baba mai kanwa yamin...... Kwanciyarta tayi tana cewa, “idan kinga bazaki iya fad'aba kibar abinki arai yayta cinki, daga k'arshe idan kika rufta auren ya tsinke kekika Sani, kinsandai minene wannan gidan da irin mutanenen cikinsa, dama kullum burunsu kenan”. Idona cike da kwalla na kamo hannunta, “kiyi hak'uri sweetheart tashi muyi magana”. Munubiya taiyi kamar ta shareta saikuma ta tashi tana share mata hawayen dake bin fuskarta. Ta gyara zamanta tana fad'in “wato Munubiya.................🤫✍🏻 Kumuje zuwa page nagaba my guys😉🤩. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu👏🏻😭_* *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻 1⃣3⃣ ..............“Wato Munubiya abinda yasa kikaga inata 6oye miki shine, bansan manufar mahaifiyarsa ba kai tsaye, nidai bayan tabani tarihin masarautarsu takuma rok'eni nabama Galadima gudunmawa wajen saka idanu akan motsin kowa dazai mu'amulanceni, abinda ta lura shi yafi maida hankalinsane ga mak'iyan waje, gani yake kamar a masarautarsu babu mai iya cutar dashi. tace min Galadima bashi da yarda ko kad'an, sannan mutumne mai zama akan ra'ayin kansa, tankwarashi sai ita da baya iya bijirema umarninta”. “Na damu kwarai da gaske Munu.. Dan rayuwa da irin mai wannan halin yanada wahala, musamman mutum mara yarda, wlhy nadad'e a gidannan bai bar zargin an turoni Na cutar dashi bane, saida Momma tafara koyamin dabarun zama dashi, tace nadaina jin tsoronsa, inhar yafad'amin magana Na daurema zuciyata Na dinga maida masa murtani, a tak'aice dai nake masa tsiwa. A lokacin da taimin wannan maganar abin yaban mamaki, Yaya uwa za tace aringama d'anta rashin kunya ko rashin raga masa?, kema kinsan bawai bazan iya baneba, amma yanamun matuk'ar kwarjini, bansan kuma miyasaba nakejin shakkarsa a zuciyata, har gobe idan yamin Abu zan maida masa murtani wlhy saina dage saboda tsoro. Saida zamanmu yad'an fara nisane Na fahimci abinda take nufi, inda bana nuna masa banida tsoroba zansha wahalar zama dashi, sannan bazai ta6a aminta dani ba ya saki jikinsa, zaita d'aukatane a y'ar lek'en asiri, Dan babu abinda ya tsana irin karinga masa Abu kana nuna tsantsar biyya da kwantar masa dakai, shi a wajensa kazo cutar dashine kawai. Maganar zuwana wanka itace tadage akan sainazo, sannan tace duk zuwan da zaiyi wajena Na nuna masa cewar. nifa bazan koma gidansa ba, dan bazan iya da hallayarsa ba, tadai nunamin dukkan dabarun dazanbi Na dinga zungurinsa da zancen, to ni wlhy ban fahimci manufartaba, tunda nasan babuma Wanda yasan mafarin ginin auren namu, daga ni sai shi, saikuma ke dana sanarmawa. yau kuma namasa zancen rabuwarne da nuna masa zan shayar dasu Abdurraheem ne Na wata shida nayi aurena nima, shinefa yahau kaina da bala'insa, wai babu wawan daya Isa shi ya k'etara gona wani yako ra6eta, koda kuwa ace gonar ta jinginace, inkuma hakan ta faru kobaya numfashi bai yafeba”. Munubiya ta zaro ido waje Dan mamaki, saikuma ta tuntsure da dariya harda rik'e ciki, galala nayi ina kallonta, danni banga abin dariya ananba. Saida tayi mai isarta sannan ta zauna dak'yau tana fad'in “yi hak'uri sweetheart, wlhy mijinkine yabani dariya, amma anya kuwa mahaifiyarsa batasan manufar aurenkuba?”. “Ta ina zata Sani Munu.., shidai wlhy nasan bazai fad'aba, Dan nakula yanada masifar zurfin ciki, balle yasan abinda yay bamai k'yau bane, tunda a al'adarmu da addininmu hakan ba tsarinmu bane, nadad'e ban iya fahimtar matsalarsaba, saikuma naita tambayarsa yamin banza, sai daga bayane naringa Neman dabarun samo kansa harya sanarmin da damuwarsa”. “Eh bank'i ta takiba, amma a ganina koshi bai fad'a mataba kina ganin Muftahu bazai fad'aba? Nifa tun pills daya zuba muku nafara zargin anya bada k'yak'yk'awar niyya yayi hakaba?”. “Kai Munu.. ALLAH bana tunanin haka, gani nake kawai itama da tata manufar, Dan batason halayyarsa ta shiru-shiru d'innan da k'untata kansa dayake akan yawan damuwa kodan ciwonsa, Dan tace min ciwonsa Na yawan motsawa a baya saboda yawan shiga damuwa da yakeyi, gashi bazai yarda kowa yasan matsalarsa ba saboda tsatstsauran ra'ayinsa, itakuma bataso Dan abaya yanda kikaga Sauban k'animsa da faran-faran haka shima yake, amma tunda ya fahimci miya kwantar da mahaifinsa saiya canja musu gaba d'aya, maganar ma saiya gadama idan kayi yake amsaka, abinda Na lura yanzu kuma wannan abun yarigada yazame masa jiki gaskiya”. “dukna fahimceki Munaya, amma abinda Na lura kamar wata alak'a mai k'arfi da kusanci takeson ginawa tsakaninki dashi, Dan babu wata uwa dazatasa matar d'anta ta ringa ma yaronta rashinkunya, itakuwa tasan halin d'anta ciki dabai, tanada dabarun dazata d'oraki domin shi su k'ayatar dashi harya ringa kallonki a matsayin mata ba auren wucin gadiba, dukkan maganganun daya fad'a miki d'azun wlhy Na mutumne mai nuna tsantsar kishi, ALLAH ma yasoki dabakizo da kumburarriyar fuskaba wlhy”. ta k'are maganar da sanya dariya. Harara Na zuba mata ina fad'in “nikuma kamar wata sokuwa saina zauna ya dakeni, danma gaskiya shiba mutum bane mai yawan saurin hannu, saidai k'asaita da shariyar tsiya, kaita magana yayi tamkar bai jikaba”. “Yo Sweetheart ai mulkin kenan ko, wannan shine ake kira sarautar, idan bashida wannan izzar da k'asaita lallai baicika jinin basarakeba, shi nashi ai da sauk'i tunda yasan darajar d'an Adam. Amma lallai ki godema ALLAH da samun suruka irin wannan, to amma ke kina sonsa yanzu?”. Harararta nayi, nazame Na kwanta batareda Na bata amsaba, ta d'akamin duka a cinya tana fad'in “Munafuka kema sonshi kike, wannan jan ajin naku dukshi ke cutarku, shi mulki ya hanashi ya fad'a, ke shegen jan aji yahanaki ki nuna masa, basai kuyitayiba har yaranku su taso su ganku a haka”. Baki Na murgud'a mata ina Sosa wajen data dokenin, Dan naji zafi, cikin harara nace, “ai ba a haifi namijin dazan fara furta masa ina sonshiba koda ace son nasa zai halakanine, k duk taurin kai da miskilancin Yaa Marwan ince saida yace yana sonki sannan kika amsa masa?, saini kikeson Na zubar da tawa darajar, salonma ya d'auka kwad'ayine ya sakani hakan, zai ru6e kuwa inhar jira yake sainace Sameer ina sonka, bank'i idan naga zan iya nabika ta wata hanyarba, amma shida yace auren Contract shine zai dawo ya gyara kuskuren da yayi da kansa, shiyyasa nake son canja masa tunaninsa ta hanyar tunatar dashi yasan mace tanada daraja, ba'a sakata lokacin da akaso sannan ayi tunanin cirewa lokacin da akai niyya, wadda batasan darajar kanta bace zata amince da hakan, nikuma bana cikinsu danba Auren kwad'ayi nayiba”. Munubiya tayi dariya tana jinjinamin, “yayi k'yau gimbiya matar Sarkinmu mai jiran gado, wlhy kin burgeni dan wannan shine kima, amma dai a sassautama galadimanmu, Dan naga alama shimafa ya zurma fad'arce kawai mai wahala a harshensa, amma mizai hana mubi wasu dabarun Dan bud'e bakinsa”. “babu wasu dabaru dazamubi sweetheart, Dan nidai bazanbi ta hanyar talla da jikina ba a gareshi danya soni, randa Na tsufafa? K'yawun jikin ya 6ata ko Na nakasa?, bazanbi ta yaudaraba ko wani kwarkwasa, randa yaga wadda yakeso tsakaninsa da ALLAH fa? komai zan masa bazai birgeshiba, Dan soyayya ta gaskiya daban take, baruwanta da k'yau ko k'yale-k'yale, zandai iya k'yautatama zuciyarsa domin dukkan zuciya tanason mai k'yautata mata, amma son gaskiya nakeson mijina yamin, bana k'yalek'yalen duniyaba, ko tsufa ya kamani bazai bar sonaba, ko nakasa ta kamani bazai bar sonaba, ko babu dukiya tattare dashi bazan gujesa ba, idan ciwo ya kamani koya kamashi zamu tattali juna saoda tausayi da rahamar dake cikin Auren da soyyar gaskiya da mukema juna, ko kishiya yatashimin nasan son gaskiya yakemin bazan ta6a saka kaina a matsananciyar damuwa ba tunda inada yak'ini akan son gaskiya yakemin, bazai ta6a tozartaniba, sannan ban Isa hanashi yaso matarsa ba Dan ni yana sona, nafison amin komai tsakani da ALLAH bada yaudaraba kema kinsani, Dan haka muyitayi inhar bai gajiba nima bazan gazaba”. “Duk mace haka yakamata tasan darajar kanta, takumayi abinda mijinta zai sota son gaskiya Munaya, wannan k'arancin soyayyar ta gaskiya da Muke fuskanta ayanzu shineke yawan ruguje rayuwar aure, mafi yawan mazan sukanso macene domin wata halitta ta jikinta, dasun sami nutsuwa dake kuma shikenan haskenki ya dusashe a idanunsu, wasu kuma Matan mai dukiya ne hangensu ko k'yau, da zarar mijin yazo babu saikiga wuta ta tashi, kokuma bashi dashi dama duk k'aryane, dakinje bakiga abinda kika aureshi danshiba babu sauran zaman lafiya kuma, gaskiya muna cikin matsala yanda taron biki yake a wannan zamanin kawai ya Isa ruguza dukkan albarkar aure, amma ni dazakiji ta tawa tunda shima yana sonki kubar wannan 6oyewar mana”. “Munu, idanfa bai canjaba nima bazan canjaba, bakinsa daya furta shi nakeso ya gyara da kansa”. “lallai to sai kiyita 6oyewar, idan ya nemi kasheku duk zaku fiddoshine kowama yaji, ai nama godema ALLAH da Muftahu dan ta silarsa ALLAH yamuku dabaibayi da yarannan, Ubangiji sarkin hikima kenan, naga Wanda zai iya barma wani ai”. Banza namata nayi kwanciyata, harma barci 6arawo ya saceni. Munubiya ta d'auki wayar munaya tana murmushi, tayi abinda zatayi ta ajiye mata abarta itama ta kwanta. ★★★★ Galadima daketa juye-juye a gado abin duniya dukya ishesa saijan tagwayen tsaki yakeyi ya kalli wayarsa datayi alamar shigowar sak'o, harzai share dai saiya kasa, dan numbers d'in cikin wayar duk masu muhimmancine. Jawo wayar yayi ya danna ta kawo haske, hoton y'an uku ya bayyana a screen d'in, saida yad'an ja wasu Seconds yana kallon yaransa sannan ya bud'e massage d'in, ganin wadda ta turo sak'on sai mamaki ya kamashi, Munayar da inhar bashine ya kirataba bata ta6a d'aukar waya ta kirashiba ita, amma yau itace harda message? Dukda baiyi tunamin samun mai dad'iba haka yabud'e dai, yasan bai wuce maganar data damu mutane da itaba... _Ina fatan ka koma gida cikin aminci da farinciki? Yaranka namaka fatan alkairi da addu'ar samun k'yak'yk'yawar Nutsuwa mai tarin hak'uri._ ya dad'e idonsa akan wayar yana kuma bitar sak'on, baisan murmushi ya su6uce masaba, watoma yaransa ba itaba?, kai jan ajin yarinyarnan yayi yawa, da ace agidan sarauta ta fito lallai bayi da hadimai sunga takansu, ya ajiye wayar yana gyara kwanciya, jiyay zuciyarsa tayi sakayau, dandanan barci ya d'aukesa, dama video call yayi dasu Momma, dan tun bayan daya sauka bai kuma kiransu ba saboda yau ya yini busy, ga tunani sunma kansa yawa, Munaya tagama saitashi yad'an samu nutsuwa amma shine takuma hargitsoshi da abinda zuciyarsa bazata iya d'aukaba. .............. *_Washe gari_* Munaya dai batasan minene ya faruba, dan Munubiya goge sak'on tayi bayan ta tura, da safe kuma ko alamar tayi wani Abu bata nunama Munaya ba. Wajen tashin hantsi saiga Aunty Salamah tazo, cikin farin ciki duk muka mak'alk'ale mata, ta rik'e baki tana fad'in “oh ni, ALLAH yabani y'ay'an da basu San sun girmaba”. Innarmu tace, “wlhy kuwa salama, baki moreba kam”. Laraba dai tanata musu dariya. Kayan gyaran jiki Na musamman Aunty salamah ta kawo musu, takuma bisu da gargad'in wlhy kowa tazage tayi, harda rok'on laraba ta saka musu idanu Dan ALLAH. Gaba d'aya yau a gidan tama yini, hakanne ya d'aukema Munaya damuwar data tashi da ita. ★★★★★★*★★★★★★ Tunda yadawo salla ya koma barci, saboda jiya bai wani samu yin isasheba, wajen 10 ya farka, brush kawai yayi yazo ya zauna yana hada wasu takardu, sosai aikin ya d'auke hankalinsa saboda muhimmancinsa, sauban datun d'azun yay shirin tafiya yagaji da jiran fitowar Galadima Dan haka yazo yaymasa knocking, Dan yanason biyawa wajen Munaya kafin ya wuce. Galadima dake zaune bakin gado ya baje takardu yana kuma rubutu a jikin wasu ya d'aga kai ya kalli Computer d'in dake hasko masa dukkan CCTV camera's d'in sashen nasa, ganin Sauban ne sai ya d'auke idonsa yace ya shigo. Zama sauban yayi saman stool d'in mirror ya gaida Galadima, hankalinsa nakan aikin dayake ya amsa. yace, “Dama katashi?”. “Wlhy Yaya tun d'azun Na tashi, naga baka fito baneba gashi inason kafin Na wuce nabiya Na gaida Aunty gimbiya naga my Triplet's kuma”. Galadima baice komaiba, sai had'e takardun gabansa daya shigayi, Sauban yamatso bakin gadon yana tayashi, saida suka gama tsaf, ya shiryasu cikin wani k'aramar briefcase sannan ya kalli Sauban dake zaune, “Mik'omin System d'incan”. Sauban yad'an marairaice fuska cikin tausayawa. Yace, “haba yaa Sam kad'an huta mana”. Da mamaki Galadima yace, “to idan Na huta kaine zakamin aiki?”. Girgiza kai Sauban yay alamar a'a. Ya tashi ya d'ako masa. Kar6a Galadima yay yana girgiza kansa saboda ganin yanda Sauban keta 6ata fusaka, a zuciyarsa yace bazaka fahimtaba yaro. Batare da sake kallonsa ba yace, “yanzu mikake buk'ata kenan?”. “yaa Sam kud'in wajenafa basuda yawa”. “Humm” Galadima ya fad'a hankalinsa akan aikinsa. yace, “Aikai dama baku iya tausayin kud'iba kai da Samha, mutum yarasa uwar mi kuke saya? Kaje zan turo maka, Dan yanzu kama nima buk'atar kud'in nakeyi, gashi sunyi cak, nasan kuma daga inno har papi idan suna dashi baka zasuyi”. “shikenan yaya, amma Dan ALLAH ko kad'anne”. “ka duba cikin kayan dana cire, maybe ka samu”. “yauwa Yaa Sam d'inmu. ALLAH ya k'ara girma”. Galadima Dai baice komaiba, ya kwaso kud'in duka yana fad'in “na kwashe duka?”. Kai kawai Galadima ya d'aga masa. Sauban yazo ya rungume Galadima ta baya yana godiya, sannan ya sakesa. Murmushi Galadima yayi yana fad'in “ALLAH ya gyaraka Sauban”. “Amin yayana”. Sauban ya fad'a cikin dariya. Sunyi sallama ya tafi akan cewa shima saiya zo, yakuma gaida su papi. ***************** Munaya taji dad'in ganin Sauban, sund'an ta6a hira sannan yamata sallama ya tafi tana shaida masa ya gaida mata su inno da k'yau, har k'ofar gida ta rakoshi, dukda dai bata fitoba iyakarta jikin gate, saida yashiga mota sannan ta koma ciki, tanamai jin k'aunar ahalin Galadima har cikin ranta. ************\/********** Galadima na shirin fita kira ya shigo wayarsa, saida yagama d'aura belt d'in da yakeyi sannan ya matsa gaban gadon ya d'auki wayar, a dai-dai lokacin kiran ya kuma shigowa, ganin Sir Isa saiya d'aga. Ko gaisuwa basuyiba yace, “yalla6ai kaga kuwa aika-aikar da ake neman mana?”. “Aika-aika kuma? Tami?”. “Tabbas ansaka wani yamaka kutse cikin Computer, Nazatama kagani?”. Gaban Galadima ne ya fad'i babu shiri ya yanke wayar, system d'insa ya jawo ya zauna bakin gadon, “innalillahi...” Yashiga ambata zufa Na tsatstsafo masa saboda abinda yagani Na shirin faruwa, ya manta daya gama aiki bai saka security a matakin farkoba, saurin sakawa yayi, dukda yasan babu tabbacin zai iya dakatarwa ahakan kawai da yayi, ya ajiye lap-top d'in yana mik'ewa da hanzari, sauri d'aukar rigarsa yayi ya saka, yana saka bottoms d'in a tsananin hanzarce, haka dai ya k'arasa shirin a gaggauce, ya d'auki abinda zai d'auka yafito, babu gaisuwar Wanda ya amsa, hannu kawai ya d'aga musu yanufi mota yashige da kansa yaja ya fice daga masarautar, Wanda yatafi kiran Sarkin Mota duka iso tare, duk mamaki ya kamasu, yau Galadima da kansa yaja mota, anya kuwa lafiya?. Ganin wannan bazai musuba sarkin mota ya shiga mota shima ya bishi. Yana tuk'i suna waya da Vijay abokin aikinsa Na India, a haka ya iso gidansa dake bayan gari, kusan lokaci d'aya suka Isa da sarkin mota, ganin Galadima zai fita ya bud'e gate da kansa, shi saiya kashe motar dayake ciki da sauri ya fito yazo ya bud'e masa ya shige, bai bisaba, tunda Alhmdllh yaga dai inda yazo, maybe kuma baya buk'atar kowa a wajene shiyyasa ya buk'aci tahowa shi kad'ai. Wani d'aki dake cikin bedroom d'in gidan ya bud'e ya Shiga, bazaka ta6a tunanin akwaima d'aki a wajenba, da y'ar k'ura a d'akin, amma hakan bai damu Galadima ba a yau, k'yallen da aka rufe kujeru da Computers d'in d'akin yashiga yayewa, da sauri ya fito zuwa can bayan d'akunan, yad'anyi ajiyar zuciya saboda ganin Gen... d'in gidan akwai fetur, dayake yad'an zazzo gidan kwannan, tadawa yay ya kuma komawa cikin gidan, ya kunna komai sannan ya zauna a kujera, medical eyeglasses ya saka, idonnan yayi jazur saboda 6acin rai, duk jijiyoyin kansa sun mimmk'e, hakama gashin jikinsa, kallon farko zai tabbatar maka ran maza ya 6aci. Koma a yanda yake sarrafa Computers d'in. Abinda ke kunnensa kawai naga ya danna yanayin kwatancen d'akin da za'a sameshi. Mintuna 3 tsakani saiga Sir Isa da Baffi sun shigo, saikuma ga Sauban Wanda harsun d'auki hanya Muftahu ya kirashi akan ya dawo, dole ya dawo masarauta, shine suka fito shida Muftahun. Sir Isa da Sauban duk zama sukayi, Galadima Na Sanar musu abinda zasuyi. “Gaskiya shegene guy d'innan yalla6ai, wlhy yasan Computer, kagafa yana Neman lalata mana dukkan security d'inmu.......”. ‘hankali tashe sir isa yake magana. Sauban kam har kwalla ta cika masa ido. Galadima baice komaiba, aikinsa yake iya iyawar k'arfin zuciya dana k'wanji. Sai Baffine yad'an bubbuga kafad'ar Sauban yana fad'in “ka kwantar da hankalinka Sauban, insha ALLAH bazasuci nasaraba, kacigaba dayin komai a nutse kaidai”. Sauban ya kad'a kansa yana share hawaye. Galadima dayay zufa sharkaf ya kalli Sir Isa, yarigada yaci k'arfinmu kafin muzo, k'ofa ukuce kacal ya rage masa bud'ewa yasamu dukkan komai, abinda zamuyi mu bud'e masa sauran kawai, bayan yashiga ciki insha ALLAH inada wata dabara”. Muftahu yace, “Amma Ranka ya dad'e hakan riskine gaskiya, idan kuma shi yanada plans akan hakan fa?”. “Gaskiya ka fad'a Muftahu, amma hakan shine kawai hanya mai sauk'i da zamubi, inhar muka bari harya bud'e da kansa lallai zai lalata komaine, Dan wannan shine shirinsu”. Sir Isa ne mai maganar. Galadima ya danna abin kunnensa yana fad'in “Vijay mubashi dama kawai, a lokacin daya shiga kaikuma ka tabbatar da ka zuk'e dukkan nasa shirin, ga wata akwatinan dayake yawo da ita a bayan handle d'in Computer d'insa, karka ta6ata Dan makircine ya shirya a cikinta, munayin kuskuren ta6awa labari zaisha Banban. Alex yay gaggawar had'amin sabbin Securitys muga kozasu ja hankalinsa can, ga hoton yaranan zan d'ora masa, dasu zaiyi amfani, dan dolene mu kauda masa hankali, yasan mi yakeyi sosai”. “Ok! Ok! muje zuwa kawai” vijey ya amsa a hanzarce. Da sauri Galadima ya maida kallonsa ga Sauban yana fad'in “dakaje duk ka d'auki su Amaturrahman ne?”. “Eh yaya dukna d'aukesu”. “A lokaci d'aya ko daban-daban?”. Na d'aukesu lokaci d'aya, nakuma d'auki kowa shi kad'ai”. “Alhmdllh taso nan”. Tashi Sauban yayi ya matsa inda Galadima yake, wani glass Galadima ya tura masa, yace, “'Dora duka hannayenka anan mugani”. 'Dorawa Sauban yayi, bayan ya ta6a wani farin Abu da Baffi ya bashi, shatin hannun yaran suka bayyana, dayake yayi musu wasa sosai, amma kuma hakan bazai gamsarba. Daga can Alex yace bazaiyiba, dole akawo yaran. Shima Galadima ya tabbatar bazaiyinba, sai hankalinsa ya kuma tashi, yaran sunyi k'ank'atar daza'a fito dasu daga gida. Muftahu yace, “Ranka ya dad'e bara kawai naje Na kawosu inaga zaifi sauk'i”. Baffi yace, “hakan shine kawai dai-dai sai dai bakai yakamata kajeba, a kira mahaifiyarsu tabama Wanda zai iya 6adda bamanni wajen kawosu, kuringa tunawa sumafa idonsu nakan kowane motsinmu a yanzu, shiyyasa tun a jiya naima Sameer hannunka mai sanda akan hakan”. Galadima daya zubama Computers d'in ido kawai yana kallon 6arnar da ake shirin masa. Ya mik'e tsaye yana fad'in “Muftahu ka kira mai taxi d'innan yaje inda yata6a ajiyeta za'a kawo masa yaran”. fitowa yay daga d'akin yana k'ok'arin neman number Munaya ya kira. Bugu biyu Munubiya da wayar ke hannunta ta d'aga, tana mannama Munaya wayar a kunne, bai amsa sallamarta ba yace, “Yanzunnan ki bama Innaro da laraba su Abdurraheem, sufito bakin layinku akwai mai taxi zai d'akkosu”. Cike da mamaki Munaya tace, “yalla6ai ban ganeba?”. A tsawace yace, “basai kinganeba, Dalla malama kibasu karki 6atamim lokaci”. Sosai Munaya ta tsorata da tsawar tasa, kad'an yarage wayar ta su6uce mata ta daiyi azamar rik'ota, batada za6in daya wuce bin Umarninsa, dukda hankalinta bai kwantaba da hakan. Yanda yace ayi haka tayi, innaro da laraba Na fitowa suka samu mai taxi yana jiransu. Cikin mintuna k'alilan suka iso, Muftahu da Sauban sukazo suka kar6i yaran, akabar su innaro a mota zasu jira. Akan wani Abu akad'an d'orasu, da hotonsu ya fota a Computer d'in sai'a ciresu, sud'uka duk aka d'ad'd'orasu, sannan su Muftahu suka maidasu wajensu innaro aka koma dasu. Sudai duk mamaki ya cikasu akan miya faru? Basuda mai basu amsar wannan lamari. Bayan su Galadima sun turama su Alex hotunan yaran sai duk suka koma gefe suka zubama Computers d'in ido, sauran lamari sunbarma ubangiji. Suna kallo wancen ya shige inda yakeso, bayan sun bashi dukkan dama, tashin hankalin Galadima shine, mutumin lalata komansa yakesonyi bawai d'auka ba, idan da ace d'aukace hakan mai sauk'ine, k'iris yarage wancan ya cinmusu, Galadima ya lumshe idonsa zuciyarsa Na k'una yana ambaton sunayen ALLAH, abinda ya d'auki tsawon shekaru yana tanadinsu ga wani banza zai gogesu cikin seconds, hakan ya tabbatar masa da Harun ne yabada wani yanki Na sirrinsa, saboda yasan abubuwa da yawa akan aiyukansa, sauban ma k'asa yay dakai yana hawaye, shikenan dukkan hujjojinsu da suke ganin zaisa su samu a hukunta masu laifi suntafi, baffi da sir Isa da Muftahu ma duk jikinsu yayi sanyi, kowa sai zuciyarsa Ce ke bugawa...... Sauban yace, “Yaa Sam!”. Galadima ya tashi zaune sosai yana bud'e ido da kallon Sauban, batareda ya amsaba. Sauban yace, “yaa Sam mizai hana mu gwada dabaran kashe Computers d'insu, kaga seconds 30 kawai yarage ya cimma burinsa”. Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, murya a sark'e yace, “Sauban abinda ya rage mana yayi kad'an wajen yin hakan, kuma zamu iya kuskuren da komai zai goge d'in da kanmu, kubarsa kawai yayi yanda yakeso......” Katseshi baffi yay da sauri, “Sameer mu gwad'a d'in kawai, maybe a samu dacewa”. Badan Galadima yayi tunanin samun nasaraba yatashi zaune jiki a sanyaye yana dannawa, Sauban yakuma fad'in “yaya Please kayi da yak'ini, saura 20 seconds fa”. Tamkar Sauban yayima Galadima allura ne, yafara komai cikin hanzari, yayinda sir Isa ke taimaka masa. Muftahu da Baffi dai y'an kallone, Dan basusan komai dangane da wannan harkarba. Saura second 1 ya rage Galadima yasamu damar kashe Computers d'insu dana wad'ancan. Suda ke murnar samun nasara duk sai sukayi tsit, su Galadima kuma Sauban ya sanya ihu. Hararsa Galadima yayi, yayinda su Baffi sukai dariya. Dukda suna addu'ar samun nasara hankalinsu bai kwantaba, Dan sai an kunna Computers d'in zuwa wanu lokaci, idan an tabbatar da samun nasara sannan. *************** Hankalim Munaya bai kwantaba saida taga su innaro sun dawo k'alau, babu kunya taita d'aukar yaran tana jujjuyawa wai kozataga wani abinda aka musu, saidai kuma bataga komaiba. *************************** Baffi ya kalli Galadima dayay shiru ido a lumshe, yace, “Sameer dolenefa komai yazo k'arshe yau, kabi ta hanyar da katsara domin zuwansu hannu gaba d'aya, daga baya saimu cigaba da Neman camera, dan Na tabbata bazasu hak'ura ba, shiyyasa tun a jiya Na sanarmaka”. Galadima ya jinjina kansa batare da ya bud'e idoba yace insha ALLAH komai yazo k'arshe Baffi, safiyar gobe zaku tashi dajin yanda ta kasance, Nuren yana hanyar dawowa. Zamu tafi matakin k'arshe yau”. Atare suka had'a baki wajen addu'ar ALLAH ya bada nasara. Galadima ya amsa akan la66a da amin...............✍🏻 Lallai gobe da kallon kenan. Galadima manmu ka cika musu aiki kawai🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼 *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _________________________ _Masoyan RAINA KAMA... Alkairin ALLAH yakai gareku aduk inda kuke❤❤❤❤, bilyn Abdull nayinku fiye da yanda kukeyinta._ *TASKAR LITTATAFAN HAUSA*😘👌🏻 *ZAUREN HASKE*😘 *KUNDIN HASKE*😘 *RAINA KAMA FANS CLUB* GROUP 1,2,3,4,5 duka Na gaisheku, Wanda Na bud'e da Wanda masoya suka bud'e, inayinku over wlhy, I love you irin Trillion's d'inan fa🤸🏻‍♀😘. *ZUREN BIEBIE ISA*😘👌🏻 *NICE N COOL NOVELS*😘 *PHARTY NOVELS*😘 *HUGUMA CONVERSETION*😘 *RANO NOVELS* 😘 *MANSHAT NOVELS*😘 *XUMUNTA NOVELS*😘 _Aradun ALLAH kunada matuk'ar yawa, gashi bana kusa balle naita jeroku babu gajiyawa, ina missing naku gaba d'aya, irin babu dad'i d'innan😔😂._ I love you all irin manya-manya d'innan😘😘😘😘😘😘😘🤸🏻‍♀👌🏻 __________________________ *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣4⃣ .................Duk da dai sumbar komai a halin k'ila wa k'ala haka kowa yafito jiki a sanyaye, Baffi da Sir Isa suka wuce, Galadima ma kallon Sauban yayi daya zuba uban tagumi, yad'an murmusa yana fad'in “Haba autan Momma, miye kuma Na damuwar haka? katashi kuwuce kawai kar yamma tayi”. Shagwa6e fuska Sauban yayi yana kallon yayansa, yace, “please Yaa Sam kabarni sai gobe saina wuce insha ALLAH”. Galadima yay shiru alamar tunani, saikuma ya girgiza kansa, “uhm-uhm Sauban ka wuce yau, Dan gobennan akwai riski”. Kamar Sauban ya tambaya dai amma yay shiru, yasan halinsa mawuyacine ya sanar masa. Dan haka saiya amsa da to kawai. Badan yasoba yaymusu sallama shima driver dazai kaisa yad'aukesa suka tafi. Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, zuciyarsa Na k'una da tsantsar damuwa. tausayinsa ya kama Muftahu dake zaune shima yayi shiru damuwa da tausayin d'an uwan nasa fal ransa. ★★★★★★ Gaba d'aya zuciyar Munaya takasa sukuni gameda yanda taji muryar Galadima, tunda kuma aka maido yaran saita kasa zaune ta kasa tsaye, Munubiya dai da innarsu duk suna hankalce da ita, kamar Munu zata shareta saidai tamata magana. “Nikam aganina da wannan zagaye-zagayen da kiketayi Sweetheart ai gara ki kirashi kisan damuwarsa, koma ladan kwantar masa da hankali k'yasamu”. Munaya dake kwance akan gado ta kifa meenal saman cikinta datai barci ta kalli Munubiya, amma sai munu ta basar tamkarma ba ita tayi maganarba. Ajiyar zuciya Munaya ta sauke, yayinda Munubiya ta tashi tamayi ficewarta daga d'akin duka, harta fice Munaya nabinta da kallo, saida tabar ganinta sannan ta janye idonta a k'ofar tana cigaba da shafa bayan meenal. Shawarar Zuciyarta dake cigaba da k'arfafa mata shawarar y'ar uwarta ta addabeta da k'awato mata Galadima a damuwa, da alk'awarin dataima Mahaifiyarsa. Kasa daurewa tayi saboda tausayin ahalinsa dashi kansa daya kamata, ta jawo wayar tana lalubo number sa, dukda k'irjinta Na dukan gama-goma Na tsoron tsawar daya mata d'azu da yanda suka rabu jiya. Haka dai ta dake tayi dialing number sa. Galadima suna zaune cikin halin shiru da Neman mafita a zukata shida Muftahu kira ya shigo wayarsa, sharewa yay tamkarma bai jiba, ganin zata tsinke muftahu ya taso yay picking da sauri ganin *My Mata* yasan dai Munaya Ce, a kunne ya saka masa, Galadima ya bud'e jajayen idonsa ya kallesa, Muftahu yamasa alamar please da fuska. Baice komaiba ya kar6a wayar yana maida idanunsa ya lumshe, Muftahu kuma ya fice abinsa. Munaya tayi shiru takasa magana, kamar yanda shima yak'i cewa k'ala, sai sautin ajiyar zuciyarsa take jiyowa kad'an-kad'an, daurewa tayi tace, “Assalamu alaika”. Dukda yasan itace saida yaji sanyi a ransa, Dan ita kad'aice kemasa haka a waya ya jure, saida ya d'auki wasu seconds kafin ya amsa sallamar. Yanda ya amsa sallamar kawai ta tabbatar akwai matsala, Cikin aro jarumta tace, “Ranka ya dad'e barci kakeyi?”. Yad'an murmusa, a zuciyarsa yace yarinyarnan a kwai wayo, “Uhm-uhm”. ‘yafad'a a sanyaye’. Ganin tafara samun dama saita kuma saita muryarta tace, “'Dan gatan Abie, to mikakeyi ne haka? naji muryar taka can k'asa”. Zamewa Galadima yayi ya kwanta cikin kujerar, yanzunma tamkar bazai amsaba, saida ya gama basarwarsa sannan yace, “k mikikeyi?”. Munaya tayi murmushi mai sauti har yana jiyowa, ta shafa kan Meenal tana fad'in “kwance kawai nake ina tunanin rayuwa da abinda ta k'unsa, harma da Wanda ke gudana a cikinta”. Yace, “Humm kamar mikenan?”. “Kanason ji?”. Ya kuma cewa “Uhm”. “humm yalla6ai nakula duk yanda bawa yakai da samun komai Na rayuwa saikaga wata damuwa ko tawaya mai kutse acikin al'amuransa, bana manta maganar nan taka da kata6a fad'amin wani lokacin murmushin da jama'a kanyi iyakarsa fuskane, amma zuciyarsu sune kad'ai sukasan sirinta, lallai wannan gaskiyane, amma kasan mike birgeni da k'aramin k'warin gwiwa a rayuwata koda ace Na tsinci kaina a fagen sanyin jiki?”. Galadima yace, “uhm-uhm”. Munaya ta sauke wata sassanyar ajiyar zuciya da Galadima yajita har cikin ransa, yayinda wani Abu ya tsarga masa ta cikin kai har zuwa yatsan k'afa, ya gyara kwanciyarsa yana jiran jin mizatace. “Komai girman fad'uwa inhar da yak'inin HAK'URI dana k'arfin ZUCIYA to lallai akwai tagomashin sirrin samun NASARA, hak'uri da juriya basa ta6a zama fad'uwa, inhar kaga bawa yayi hak'uri babu kuma NASARA a ciki to lallai hak'un nasa kad'anne, sometimes gaggawa aikin shaid'anne, saikuma ansha wahala ake shan dad'i, abinda kawai muke kasa fahimta shine riba akan sameta ne a muhalli biyu, walau a duniya kokuwa a lahira, duk wadda bawa ya samu sunanta nasara, amma kowa yafi fata da samun ta duniya, saidai ta lahira ita yakamata mufi d'oki da addu'ar samu, meybe tazame mana tsani Na zuwa inda bamuyi zatoba, hikimar Ubangijice yabaka nasarar anan kokuma a can, Dan babu yanda za'ayi a zalunceka mai kowa da komai sarkin Rahma da jink'ai ya bari, bai yarda da zalunciba, yakuma haramtashi agaremu mu bayinsa”. Wasu k'ananun hawaye suka gangara ta gefen idon Galadima, fuskarsa d'auke da murmushi, yayinda kalaman munaya ke tasiri adukan magudanar jininsa da zuciya, wata nutsuwa ta musamman daya rasa tashiga ratsashi da bashi k'arfin gwiwa, a hankali yace, “ke y'ar baiwace matar Contract”. Dukda maganar k'arshe ta sosa zuciyarta saita murmusa, cikin kuma kwantar da murya tace, “Ni a suwa Mijin contract ”. Ya d'an dara batare daya shiryaba. Yace, “one-one kenan?”. Munaya tayi dariya tana fad'in “nidai bada manufa na fad'aba”. “Fad'i gaskiya dai yalla6iya tsiwa”. “Gara mai tsiwa da miskili, koba komai akansan muna waje ai saboda tsiwarmu”. Galadima ya kuma Murmusawa. Yace, “ki kiyayi randa zan kamaki ALLAH”. Itama dariyar tayi. Tace, “yalla6ai ka fad'i wani Abu nabaka k'yauta mana”. Yay d'an jimm tunanin mikenan?, saikuma yayi ajiyar zuciya yace, “mikenan?”. Cikin wani salo Munaya tace, “R. Ita kawai nakeson ji a harshenka”. Lallai yarinyarnan taga gadon barcinsa wlhy, yay maganar a zuciya fuskarsa na k'awatuwa da murmushi. yace, “Okay, kibari sai ina gabanki”. “Tab, Indai ba yanzuba na fasa”. “uhmyim, miye na karayar hajiyar tsiwa?”. “Aiba karaya nayiba, lokacin kawai kabari ya wuce, ni karmafa yarannan suma su gadoka”. “Dai-dai kenan ai y'ammata, kokin manta k'yan d'a ya gaji ubansa”. “Humm Alfahari kenan, ita uwa an rainata”. Dariya tabashi, amma ya daure baiyiba. Yace, “keda kike gudunsu mizaisa su gadoki?”. Munaya ta d'an ta6e baki, cikin juya idanu tamkar tana gabansa tace, “yanzu kana ina?”. Murmusawa yayi saboda basar da maganar da tayi. Yace, “kinason ganinane?”. “A'a, son sani kawai nake”. “Humm, naje tad'i to”. Shiru munaya tayi, sai kuma ta d'an dara, “Yalla6ai kasan wani Abu kuwa?”. “Saikin fad'a”. Cikin danne dariya tace, “irinku kwantai kukeyifa, sai anyima y'ammata tallarku asamo mai taimakonku ta aura, kaima nasan saisu takawa sunmaka haka.....”. Sai yaji kitt, ta yanke wayar. Wani k'asaitaccen murmushi ya saki yana shafa kumatunsa, ya d'ora wayar saman cikin sa yana fad'in “lallai yarinyarnan kin girma, zaki tabbatar nayi kwantai kuwa”. Daga canma Munaya dariya taketa k'yalk'yatawa, harta tada Meenal, Mununiya datun d'azun take kallonta ta bayan labule bata saniba tayi murmushin jin dad'i itama tana share hawaye, tanason y'ar uwarta sosai, sannan wayonta da iya mu'amullarta na birgeta, tabbas Munaya tanada tsiwa, amma tanada wayo, inhar zaka takurata bazata ta6a raga makaba, amma tanada tausayi dason ganin farincikin wani koda ita zata rasa nata farincikine, gakuma son girma uwa gyambo, tanason komi zaka mata ka nuna muhimmancinta a gareka, a fili tace, “ALLAH yakawo farinciki mai d'orewa a ratuwarki kema y'ar uwata”. Amin munu😘☺. ★★★★★★★★ Tunda Muftahu ya shigo yakebin Galadima da kallon mamaki, ganin yasake yanata fara'a tamkar ba shine a matsananciyar damuwa yanzunba, ya zauna zuciyarsa na addu'ar samun mace tagari, dan lallai *MATAN KWARAI RABIN ADDINI ce*. Galadima ya hararesa yana tashi zaune, “malam lafiya ka k'uramin ido?”. Dariya Muftahu yayi sosai, yace, “to miye na tsarguwar ranka ya dad'e, wlhy kuna sha'aninku kaida gimbiyarka, yanzu nan harta saukeka daga hawa saman da kayi”. Filo Galadima ya jefama Muftahu, shikuma ya cafe yana dariya. Galadima ma murmushin yayi yana danna kiran Sauban. Dan yasan har yanzu yanacan cikin damuwa. Hasashen nasa kuwa yayi dai-dai, Dan har yanzu muryarsa a cinkushe take. Amma jin ta Galadima a sake sai farinciki ya kamashi, cike da zumud'i yace, “yaya an dace ne?”. Murmushi Galadima yayi mai sauti, yace, “muna fatan hakan autan Momma”. Alhmdllh Sauban yashiga jerowa, saiya saki jikinsa kuma harda tsokanar Galadima yana dariyar k'eta. Galadima dai murmushi yakeyi yana girgiza kai, ya yanke wayar zuciyarsa na addu'ar ALLAH ya saka farinciki a zuciyar Munaya fiye da yanda ta sakasu. Massage ya tura mata sannan ya kalli Muftahu yana gyara zama. Munaya na kwance har yanzu takasa fita, tunda tasamu Meenal ta koma barci saita lumshe ido tana dulmiya duniyar nazari, shigowar sak'one ya sata bud'e ido ta jawo wayar. Ganin Galadima ne saita mik'e zaune babu shiri, sak'on ta bud'e. _“Kin yaudareni da zance banko tambayi yaya jinin jikina sukeba yalla6iya, to ki shafamin kansu._ *_ALLAH ya sanya farinciki a rayuwarki fiye da yanda kika Sani_*. Wasu hawayen farinciki suka gangaro a kumatun Munaya, bata ta6a tunanin shirmen datake masa yanayin tasiri a zuciyarsa ba, Dan bai ta6a nuna mataba, a fili ta furta “ALLAH na gode maka dana zama sanadin saka wani bawa naka farinciki a lokacin jarabawar damuwa ta lullu6e jinsa da ganinsa da zuciyarsa”. Amin munaya, muma Ya ALLAH kabamu ikon bama bayinka muminai gudunmawar farinciki mai amfani koyaya ne, amma bata hanyar sa6onka ba ko take k'a'idar daka shinfid'a mana, amin👏🏻😭. ************************* Muftahu da Galadima suka fito, yauma bai zauna bayaba duk yanda Muftahu yaso hakan, dama yay masa maganar zama bayan hararsa yayi, dole yaja bakinsa yay shiru yana murmushi. Wani wajen cin abinci Muftahu ya tsaya, ya kalli Galadima dake kwance jikin seat ya lumshe ido yace, “ranka ya dad'e Dan ALLAH ina zuwa”. Kai Galadima ya jinjina masa kawai batareda ya bud'e idoba, Muftahu ya fita, mintuna 15 saigashi ya dawo hannunsa d'auke da ledoji, ya bud'e seat d'in baya ya ajiye, sannan yadawo mazaunin driver yana maba Galadima hak'urin jira. Baice dashi komaiba, Dan tuni yama lula wata duniyar. Gidan gonar Nuren suka nufa, inda su Harun suke a ajiye, a falo suka yada zango, ko ina k'al yake a tsaftace ga k'amshi, cikin masu kula da gidan gonar ya shigo d'auke da wankakkun y'ay'an itatuwa masu k'yau, zubewa yay yana kuma kwasar gaisuwa, Muftahu ne kawai ya amsa, Galadima hannu ya d'aga masa. Muftahu ya bud'e abinda ya siyo yana fad'in “Ranka ya dad'e mizakaci?”. Cikin d'an ta6e baki ya girgiza masa kai alamar bazaici komaiba. “Okay, to bara na kira Gimbiya meybe ita ta saka kaci”. Bud'e ido yayi yana zubama Muftahu harara, shikuma ya fuske tamkar bai ganiba. Saida Muftahu yasha fama kafin Galadima ya yarda yad'anci abinci, rabima duk fura da kayan itatuwan ne yasha. Sunkai 1hour da shigowa ya buk'aci ganin Harun da SD. Sun fara shiga d'akin da harun yake, bayan Muftahu ya saka key ya bud'e matsawa yay yabama Galadima hanya yafara shiga, takun takalmansa ya saka Harun dake zaune bakin gadon d'akin kansa a duk'e d'agowa, kallon ido cikin ido sukaima juna, Galadima ya janye nasa cike da basarwa yana wani miskilin murmushi mai k'ona zuciyar mak'iyi. Harun ma janye idanunsa yayi yanajan tsaki, Muftahu kuma ya ta6e baki yana gyarama Galadima kujerar zama. Galadima ya zauna idonsa akan harun, hannunsa ya mik'a ya kar6i lap-top d'insa dake wajen Muftahu, ya d'orata bisa cinya sannan ya janye idonsa ga harun dayak'i sake kallonsa, lap-top d'in yafara dannawa cikeda kwarewa, cikin seconds dabasufi 10 ba ya d'ora lap-top d'in saman stool d'in da Muftahu ya sake ajiyewa, sannan yay playing abinda ya kunna yana hard'e hannaye a k'irji da zubama Harun ido. Harun har yayi tamkar zai share sai dai ya kalla lap-top d'in, Wato shine a ranar sunan y'an uku gab da za'a sace yaran shida d'aya daga cikin kidnapers d'in. “Bibo inaso Ku tabbatar da kun kwashe yaran, karku kar6i wad'anda suke hannun k'annen matarsa, Dan na bogine, baby dolls ne aka sakama kaya irin na yaran domin kauda hankali, Sameer yanada wayo fiye da yanda kuke tsammani, Dan haka kuyi komai cikin kulawa da taka tsantsan, dai-dai lokacin da wutar hotel d'innan zata d'auke, zan kwashe yaran insha ALLAH, harsai nabar cikin hotel d'in ni da ku sannan za'a kunna, ina fata ka fahimta”. “Eh na fahimta ranka ya dad'e, namaka alk'awarin ko y'ay'an sarkine bana Galadima ba yau saisun kwana a alahira”. “No, banason su mutu yanzu, sai shi ubansu ya d'and'ana d'acin rashinsu, yana gab da mutuwa sai a kawo masa gawarsu, daganan shima kaga ai sai tafiya shida wannan tatsitsiyar matar tasa y'ar bayi”. “Okey nagane boss”. Mamaki ya kama Harun har Muftahu. Zuciyar Harun tamkar zata fad'o waje dan mamaki, ya akai Galadima ya d'auki wannan video d'in, bayan dukkan CCTV cameras d'in dake hotel d'in saida suka saye mai kula dasu na hotel d'in aka tsayar dasu daga aiki........ Murmushin da galadima yayine ya katse tunanin Harun , cikin lumshe idanu da kad'a kai ya gyara zamansa, cikeda izza yace, “Abin mamaki ko? haka nake ni dama, kullum cikin bada mamaki, tabbas 6oyen dakai masa bazai yuwu muganiba, saidai kamanta da koda ace banida hanyar ganin naka idan ubangiji bai k'addaro ruhi na kona y'ay'ana ko matata zai salwanta a hannunka ba babu yanda ka iya, kana tunanin duhu da tsayar da cctv d'in hotel d'in zai baka dukkan dama ko? To kayi kuskure dan Muhammad Sameer kansa cctv ne, eyeglasses d'in dake idona komai duhun waje shi zai haskokane, dan camera d'in jikinsa tana tareda komai, kasan miyasa nabaka damar d'aukar yaran? Saboda hakan yana cikin k'addararsu, nakuma barka dasune danna kafa maka tarkon neman hujja da tabbatar da abinda Muftahu ya sanarmin”. Muftahu ya d'age gira saboda kallon tsana da Harun ke masa. Murmushi Galadima ya kumayi yana cigaba da fad'in “ka kira matata tatsitsiyar yarinya y'ar bayi ko? Saikuma abin mamaki ita wannan y'ar bayin, tatsitsiyar ce ta zame maka RAINA KAMA, dan lallai gashi zakaga GAYYA. itace ta haskomin kai a cikin madubin fik'irarta tunkan Muftahu ya sanarmin, takuma koyamin yanda zan fahimci makircinka da nagartar Muftahu, tabbas na yaba ma basirarka Harun, kanada basira k'warai da gaske, tunda kasan kanka kake a jikina kana cin dunduniyata, ni matsayin aboki d'an uwa mafi kusanci nake kallonka, kamar yanda mahaifina yarink'a kallon mahaifinka, ashe kud'in duk kaskane a garemu, nayi imani da cewar lallai ku jarabawane a garemu, kamar yanda k'addarar auren Munaya tazamema rayuwata alkairi, a kullum cikin aibanta Muftahu da bak'antashi kake a gareni, ashe kaine bak'in ba shiba, mimuka muku ni da mahaifinane haka da zafi? Nawa suka biyaku kuke cutar damu.............?”. “Sameer!!”. Harun ya kirayi sunan galadima cikin fushi, ya mik'e tsaye sunama juna kallon ido cikin ido shida galadima, cikin matsannan ciyar tsanar juna. “Kabar alfahari magen matarka tamaka bajinta, shawarama zan baka ka janyeta cikin wannan hargitsin, danko ubanta daya shiga a had'ari yake balle ita karan kad'a miya, wlhy Sameer ban ta6a k'aunarka ba, bakuma zan ta6aba har abadan, domin tsakanina dakai BASHIN GABANE, dan haka banida lokacinka yanzu har sai Camera ta dawo hannunmu, bar ganina anan a rufe, akwai mai sarrafa dukkan tunanina a waje, yarage naka kanemi hanyar kare Surukinka kafin aikinmu yazo kansa...”. A fusace Galadima ya mik'e shima yana dunk'ule hannu, amma sai Nuren daya shigo yanzu ya rik'eshi, “relax my brother, kainefa ka ta6a fad'amin ba'a maidama abokin gaba murtani da murtani, sannan ba'a bashi damar sanin sirrin yak'i sai an had'u a filin daga”. Galadima ya saki hannunsa daya dunk'ule da bakinsa daya cije, yatsunsa ya kad'a suka bad'a k'ara d'as! 'Das! Sannan ya zagaya hannunsa a wuya alamar I will kill you. Cikin d'aga murya Harun yace, “d'an halak ka fasa Sameer!”. Daga Nuren har Muftahu da Galadima babu Wanda ya amsa masa, a falo suka tsaya, Galadima ya Nufi d'akin da SD yake batare da yace uffanba, Nanma dai Muftahu ya bud'e masa, ya shiga cikin tsananin fusatar da Harun ya sakashi. zauna suka iske Alhaji Darma cikin kujera yana duba jarida, kaikace a d'akinsa yake. Galadima ya taune lips nashi tamkar zai hudasu da hak'ori, zuciyarsa Na k'una, lallai sai Harun da ubansa sun k'are rayuwarsu a jail inhar yana numfashi, dan barin irinsu a duniya had'arine babba, musamman a gida irinna sarauta......... Nuren ya katse masa tunani ta hanyar yima SD magana. cikin ta6e baki Alhhaji Darma ya kalli Galadima yana wani murmushin mugunta, ya ajiye jaridar hannunsa tare da hard'e k'afa. A bakin gadon Galadima ya zauna, ya kalli Alhaji Darma, sosai Darma ya tsorata da rinannun idanun Galadima, amma saiya dake. Galadima daya lura da rikitar Darma ya murmusa, cikeda k'asaita ya d'age girarsa, “Alhaji Shehu kenan, angaya maka mutum yakanci bashi ya kwana lafiya, duk wata jarumta da zaka aro kasama ranka tuni nagama bitar karatu a kanta, karigada ka shigo ramin damusa iya gudunka babu wajen 6uya, bama duk wannan ba, minene had'inka da surukina? Sanann minene yasa kuka kashe mijin y'ar uwata? Dan ko tantama banayi da hannunka a cikin kisanshi!!”. Galadima ya k'are maganar cikin matsanancin tsawar data rikita Alhaji Darma. Dukya rud'e yarasa ina zai kama, cikin in ina yace, “Ni sharri zakaimin bansan komai akan mutuwarsa ba”. Galadima yay dariya, saikuma ya gimtse fuska. Yace, “Okay, babu hannunka amma kake tursasa yarinyarsa Samha ta dinga d'akko maka sirrikana tana kawo mata? Kullum kana ma yarinya barazana da mutuwa ko? Alhaji shehu aini tun ranarda mijin aunty Mimi zai koma ga ALLAH naga idonsa ya tsaya cak akanka lokacin da numfashinsa ke bankwana da duniya na d'ora alamar tambaya a kanka, sai kuma yanda kake kaffa-kaffa da Samha a gaban mutane, yayinda itakuma take a d'arare dakai, dukkan wayar dakake mata kana sakata sato maka sirrina INA kan sani, dan nine da kaina nake ajiye mata tagani danta tura maka batareda ita kanta ta saniba, shiyyasa na jata jikina fiye da kowa a gidanmu, duk abinda Sameer zaiyi cikin ilimi yakeyinsa Darma, koda yake bamuzo wannan matakinba, miye had'inka da surikina?”. Alhaji Darma dake a rikice saboda tsoro da tashin hankalin zantukan Galadima ya had'iye yawu da k'yar yana fad'in, “B..babu ruwanka da abinda ke tsakanina dashi kuma”. “Hummm". Galadima ya fad'a cikin cije lips, wayarsa ya d'akko ya kunna wani recording daya nad'a a wayar Darma ranar da suka kamoshi kafin su d'akkoshi. Waya yake da wani cikin tsananin fusata, “Boss wai miyasa bazamu aika shegenan barzahu ba idan yak'i bamu Camera d'innan? Tunda munada hanyar da zamubi mu kar6a d'in, Nibansan miyasa kuke cewa abishi mataki-mataki ba, kasanfa y'arshi yaronan Sameer take aure, yanada hanya mai sauk'i dazai bashi camera d'innan, shi wancan banzan Alhaji Halluru babu tsiyar da y'ay'ansa zasuma mutane, kullum sai tsarin banza yake mana”. “Karka damu Alhaji shehu, mu bashi damar k'arshe daya buk'ata, tunda ya tabbatar mana a wannan karon zai kar6o camera d'in ta hanyar matan y'ay'ansa, yana son takara, yakuma San inhar burinmu bai cigaba shida takarar Governor saidai kallo”. “shikenan boss, bara naje ance nayi bak'o”. “Ok ngd”. Galadima ya gimtse recording d'in dai-dai nan yana murmushi da kallon Alhaji Darma dake tsuma dukan jikinsa na 6ari. Cikin d'age gira Galadima yace, “wannan ma ba matsalata bace? Kasanfa shikad'ai ya isheni hujjar gurfanar dakai gaban K'uliya, shikenan babu girma babu mulkin da ake mana Homa da tak'ama dashi right? ”. Mi Nuren zaiyi kuwa inba Bushewa da dariya ba, dan yatuna Alhaji Shehu ne yafad'ama Galadima maganarnan randa suka kamoshi. Cikin Fusata Darma yake kallon Muftahu da Nuren dake dariya, ya mik'e tsaye yana nunasu da yatsa, “y'an samari lokacin dariyarku baiyiba, dan camera d'in da kuke farfagandar nema tana gab da zuwa hannunmu, kunga kuwa ai kune abin dariya”. Ya k'are maganar da kwashewa da dariya. Dukda furucinsa ya daki zuciyar Galadima bai nunaba, saiya mik'e yana murmushi da kallon Darma. Yace, “lallai kaine ka cancanci ayima dariya, indai camera ce tadad'e da zuwa hannuna”. Yana gama fad'a ya fice, su Nuren suka kuma sanya dariya, dukda yanayin Galadima ya tabbatar musu akwai matsala. Sunama Alhaji Darma dariya suka fice abinsu daga d'akin. A falo suka iske Galadima yanata safa da marwa cikin tsantsar damuwa, sai danna waya yake yana sakawa a kunne alamar Neman wani tak'i shiga. Cikin sassarfa duk suka k'araso garesa suna tambayar lafiya?. Bai tanka musuba, saboda Munaya ta d'aga wayarsa, “Abba ya dawo kuwa?”. abinda kawai yace mata kenan. A tsorace tace, “Miya farune?”. Tsawar data rikitata ya daka mata, “ya ina tambayarki kina tambayata?”. Cikin in ina tace, “Kayi hak'uri, bai dawoba”. “ya salam” yafad'a cikin dafe kai. yace, “Kinyi waya dashi? Ko kinji wani yayi waya dashi?”. “A'a gaskiya, Jiya da safe dai nayi waya dashi nida Munubiya, amma yau ko innarmu banji sunyi wayaba.......” Cikin katseta yace “kinga maza bincikamin waye yay wayar k'arshe dashi a gidanku, sannan kuma awa nawa dayin wayar”. “Okay” munaya tafad'a tana yanke wayar. Shima wata Number yashiga nema yana fad'in “Lallai akwai matsala, tunda kukaji Harun da Alhaji Shehu sun fad'a to sunsan misuka shiryama Abba, gashi nabaza su Ameer sumin wani aikin...” ya k'are maganar da saka wayar a kunne saboda daddy ya kira. Bayan sun gaisa ya tambayesa ko sunyi waya da Abba a yau?. Daddy yace, “eh da asuba yakirashi akan zai dawo yau”. Galadima yace, “Alhmdllh Dady wace number ce?”. Dady yace bara Na turo maka. Koda Galadima ya yanke wayar saiya kira baba k'arami shima, shima ya tabbatar masa sunyi waya da Abba bayan fitowa salla, Dan wannan al'adarsu Ce ko a ina wani cikinsu yake saisunyi gaisuwar safe da bankwanan kwanciya barci, sannan idan wani cikinsu yayi tafiya zai kira y'an uwansa yayin dazai kamo hanya. Hankalin su Nuren ma duk a tashe yake, balle uban gayya Galadima.............✍🏻 🙆🏽Turk'ashi, ana wata ga wata kuma🤦🏻‍♀. Lallai yaukam tura na shirin kaiwa bango🤦🏻‍♀. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻_* *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* __________________________ *_Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, ya Ubangijin Al'arshi kama mahaifin takwara (Bily s Fari) rahama, ka yalwata kabarinsa da Ni'ima, ALLAH ka yafe masa, harda iyayenmu😭👏🏻_*. _Takwara ALLAH ya k'ara mana hak'urin rashinsu, muma ALLAH yasa randa zaka d'auki ranmu muna cikin masu imani da tsoronka, da soyayyay Manzonmu ANNABI MUHAMMADU S.A.W._😭😭👏🏻 ____________________________ *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣5⃣ .................Duk da Munaya a rikice take haka tayi jarumtar danne zuciyarta, cikin hikima ta dinga bin jama'ar gidan d'ai-d'ai tana tambayar wad'anda tasan Abba zai iya kira kai tsaye, amma kowa yakance tun daren jiya basuyi wayaba, hankalinta a tashe ta sulale gidan innaro ba'a saniba, itama dai tace tun bayan sallar asuba bai sake kiranta ba. Munaya tafito jikinta sai rawa yake, kiran Galadima tayi, lokacin yana waya, tamkar zata fasa kuka ta cire wayar daga kunnen ta, tana niyyar sake kiranshi saigashi ya kirata. Da sauri ta d'aga. Yace, “yauwa Yayi waya da wani?”. Muryarta na zuga alamar tahowar kuka tace, “A'a, innaro kawai ya kira bayan sallar asubahi, amma yau koda su innarmu baiyi wayaba”. ta k'are maganar hawaye na gangarowa a kumatunta. Galadima ya furzar da huci daga can, a hankali yace, “Munaya”. Muryarta na zuga ta amsa tana share hawayen da bakin hijjab. Had'iye abinda ya tsaya masa a mak'oshi yayi da k'yar, muryarsa takuma komawa can k'asan mak'oshi, cikin sigar lallashin da Munaya bata ta6a sanin galadima ya iyaba yace, “insha ALLAH babu abinda zai faru da Abba, kiyi mana addu'a, sanan karki sanarma kowa wani Abu har inna, wayarki tazama kusa dake, Dan zan dunga kiranki idan buk'atar hakan ta taso”. Munaya takuma goge hawayen dasuka gaza tsayawa, cikin had'iye kukan tace, “ALLAH yabaku nasara, ya tsareku da tsarewarsa”. “Amin ngd”. Galadima ya fad'a yana yanke wayar. A bakin fanfo Munaya ta tsaya ta wanke fuskarta, akuma lokacinne Zarah da Siyama suka shigo kusan lokaci d'aya. d'agowa nayi Na kallesu ina k'ak'aro murmushin da musu sannu da zuwa. Saidai ayanda suka amsamin cikin sanyin jiki saina tsorata, nabaro bakin fanfon da hanzari zuwa garesu ina fad'in “Kai lafiyarku kuwa?”. Duk d'insu murmushi suka k'ak'alo, Siyama tace, “babu komai fa sis...”. Dukda ban yardaba haka nayi murmushi, sannan Na kar6i yaransu duk biyu Na rik'e ina yaba Girman da sukayi, saikace tagwaye. Daga Siyama har Zarah basuce dani Uffanba duk suka shige, kowa tanufi d'akin Uwarta. Duk binsu nayi da kallo, saida suka shige Na sauke ajiyar ziciya nima Na nufi sashenmu Ina tunanin mike faruwa? Dan alamu sun nuna akwai dai wani Abu a k'asa. Saidai bankai ga Shiga d'akinmu ba mamansu Yaa hameed ta tareni ta kar6i yarinyar Zarah. Ban musaba Na bata tundai ALLAH yasa Nima Na Haifa balle ace, na shige falonmu da d'an Siyama nima. Bayan Galadima sun gama waya da Munaya, number da daddy ya turo masa ya duba, ganin wadda yake da itace saiya gwada kira, switch up, ya ciza lips yana kallonsu Nuren da suma duk suka zuba masa idanu. Muftahu yace, “Ranka ya dad'e mu sanarda y'an sanda mana?”. Murmuahi takaici Galadima tayi, ya girgiza kansa yana fad'in “Hakan zai 6ata aikinmu, duk indama yake a safiyar yaune suka sameshi, akwai zoben dake hannunsa zamu iya bibiyarsa tanan, saidai matsalar d'aya dole sai wayarsa Na aiki, gashi number sa kuma switch up”. Nuren yace, “to mizai hana mu bincika kozamu samu daga inda Number tabar aiki”. Da sauri Galadima yace, “yes, yes Nuren, shawara mai k'yau.....” Shiru yay yakasa k'arasawa, saboda tuno da matsalar da Computers nasu suke ciki kuma, ya dafe kansa. Daga Muftahu har Nuren duksun fahimceshi, zuwacan kuma miya tuna saiya mik'e da hanzari zuwa cikin d'akin, babu dad'ewa yafito dawani k'aramin abu a hannunsa, lap-top yajawo ya manna a jiki, ya had'a da waya ya Shiga sarrafata cike da kwarewa. Zuwa can yad'ago yana kallon su Muftahu da tura musu lap-top d'in gabansu, yana sanar dasu titin da wayarsa ta daina aiki. Cikin takaici yace, “Sunriga da sun tsara komai, mubarma tunanin plan A, muje zuwa plan B kawai”. Cikin mamaki duk suka kallesa alamar miye plan B d'i?. Lips d'insa yad'an ciza yana d'age gira d'aya da buga yatsan saman bakinsa, Yace “maida hankalinmu a nemansa shine target d'insu Na farko wajen janye ra'ayinmu, plan d'inmu mukuma anan shine bazasu ta6a kasheshi ba inhar bai basu Camera d'inba, a yanda Na lura kuma yanada taurin kai shima, bazai ta6a basuba ko fad'a musu inda take. Sunada damar yin amfani da surukan senator halluru wajen turasu gida su nema musu camera d'in, kodai ta hanyar musu barazana da mutuwa, kokuma akan aurensu, ko kashe mahaifinsu, kodai wani Abu daban, shiyyasa dolene mumaida matsalarsa cikin plan B d'in”. Duksun gamsu, dukda sufa har yanzu yak'i sanar musu miyake shiryawa a plan B d'in. Cikin damuwa Nuren yace, “Amma nasan zasu wahalar dashi”. Galadima baice komaiba dan shikad'ai yasan azabar da zuciyarsa kemasa, bayason ya nuna karayarsane saboda karsuma su Muftahu su karaya, sannan koda sanyin jiki yanemi tasiri gareshi sai kalaman Munaya su masa allura, inhar yarinya k'arama kamarta zata iya tasirantuwa da abinda ta fad'a, mizai hana shima ya samu jarumta cikin tagomashin fik'irarta. Mik'ewa yay tsaye yana tattara kayansa da fad'in “Bara Na wuce, sai kunji yadda zata kaya kawai”. Basu barshi yatafi shikad'aiba, saida sukai masa rakkiya har masarauta, koda ya shige sashensa saiya kulle kansa, domin yin shiri. Hummm,🤸🏻‍♀shirya da k'yau Galadiman mu. ★★★★★★★★★★★ Abinda ya faru da Abba shine, bayan yagama kammala shirinsa domin baro inda sukaje shida S... halluru daya jashi domin masa rakkiyar tafiyar kwanaki biyu kacal. Lafiya lau suka shiga mota zasu taho, amma sai shi S... Halluru ya dakata da cewar Abba yayo gaba, shi anmasa kiran gaggawa, bai kuma kamata ace ya tsaidashiba shi, tunda ya sanarma iyalansa yau zai dawo. Da farko Abba kamar zaice suzauna kawai harya gama, saikuma tunanin yariga da ya sanarma su innaro zai dawo ya fad'o masa, shiyyasa kawai yataho, basuyi wani nisa da tafiya ba driver ya tsaya wai motar Na d'aukar zafi, ALLAH Sarki Abba, sai shima ya fita domin taimaka masa, suna tsaka da duba motarne garadan samari hud'u suka fito daga ma6oyarsu sukai ma Abba d'aukar amarya. Duk yanda yaso kare kansa ya gaza. Driver da dama duk cikin shiri yayi haka saiya hau tsallen k'arya cikin pretending yana ihun azo a taimakesu, (🤦🏻‍♀bayan yasan baza'a samu kowaba a wajen tunda jejine☹). Abba mutumne mai dagiya akan ra'ayinsa, hakan yasa duk yanda sukaso yabasu had'inkai akan zancen Camera yak'i, yama dage shi baisan Cameran da ake magana a kaiba, kuma dayaso basun tun lokacin da ake bibiyarsa da dukiya mai tsoka daya bada, amma basuda kud'in dayakai darajar camera d'in, sannan inda zai bada kodan barazana da rayuwarsa da sukasa aikaitayi tunba yanzuba daya bada, amma yasan ruhinsa Na hannun Wanda ya halicceshi, shine kuma mai kar6a aduk lokacin da yaso, inma sun kasheshi dama kwanansa ya k'arene, Dan haka subar wahalar da Kansu kawaima. Wannan maganar Ce ta fusatasu, wani ya daki Abba a baki harya fashe, dukda yaji zafi saiyayi murmuahi kawai yana kauda kai gefe. Wanda sukasa yamusu aikin lalata documents d'in Galadima Na cikin Computers ne ya ankarar dasu zoben hannun Abba akwai wata kimiya a cikinsa, wannan ne ya sakasu cire zoben daga yatsansa, shi Abba saima yanzune yasan manufar zoben, yay murmushi, Dan hakan ya tabbatar masa cewar Galadima yasan wani Abu game dashi. Duk yanda suka ringa k'ok'arin yima Galadima mugunta a sirrinsa Na Computer Abba Na kallonsu, hankalinsa kuma a tashe yake, amma jarumin namijineshi mai iya sarrafa kai aduk yanayin daya kasance, ko'a fuska bai nuna musu yana tare da damuwar abinda sukeyinba, saida Galadima ya kashe komai nasune Abba ya sauke 6oyayyar ajiyar zuciya, dukda yasan hakan ba shine nasaraba. Wanda suka saka aiki mai suna William yashiga rud'anin abinda Galadima yayi, Dan da farko yanata cika baki babu wani d'an African daya isa ja dashi a fannin ilimin Computer, bak'ak'en fatar ai a wajen su suke koyan komai, ta Yaya kuma zasu fisu Sani?. wad'annan kalamai nasa sun Sosa zuciyar Abba da sakashi cikin takaici, shiyyasa yayta jerama Galadima addu'ar samun nasara a zuciya. Yayinda sukuma wad'anda akema aiki suke kuma hurama William kai da kwanzartashi (ko kishin Kansu basayi😏, a zageku da kuma k'ask'antar daku kuna yabon mai ganinku marasa daraja🤦🏻‍♀, wata dai bahaguwar rayuwa sai bak'in fata😏🙄. Dak'ilesu da Galadima yayi ta hanyar kashe komai ya fusatasu suda William d'in, suna kuma kunna Computers d'in komai naciki ya goge, wannan Abu ya rikita William matuk'a, gashidai yagama proud d'in shi kwarone kuma bak'in fata d'an Africa ya masa kwaf d'aya, dukkan fushinsu saiya dawo kan Abba. Ana cikin haka saiga Alhaji halluru da sauran tawagar y'an group d'in, wad'anda sai yanzune suka samu k'arasowa, da farko Abba ya zata Alhaji Halluru taimakonsa yazoyi, saida yaji suna masa izgilanci sannan ya fahimci komai, cikin tsantsar mamaki yace, “Alhaji Halliru da kanka?”. Ta6e baki Alhaji Halluru yayi, yace, “zaka bani takarar Governor ne?”. Abba yay murmushin takaici yana fad'in “Tir da kai Halluru, wannan ai jahilcine, ALLAH shikad'aine ke bada mulki ga Wanda yaso, akuma lokacin dayaso,, yanzu kana nufin duk shekarun daka d'auka a jikina kai dama da manufa kake tare dani?”. Alhaji Halluru ya kuma ta6e baki yana murmushin mugunta, yace, “Alhaji Auwal kenan, ai bama zaka tabbatar da hakanba sai y'ay'anka da kansu sun d'akko min camera sun kawo, sannan mukuma kasheka a gabansu babu yanda zasuyi, yanzu haka suna gida, zuwa anjima kad'an kuma camera zatazo garemu”. Zufa ta fara karyoma Abba a dukkan sassan jikinsa, danjin za'ayi amfani da gudan jininsa wajen tarwatsa abinda yad'au shekaru yana rik'ewa amana, k'ala baice da Alhaji Halluru ba, su kuma sai kiraye-kirayen waya suke Na had'ama Galadima tarko.🤦🏻‍♀ Abba ba tausayin kansa yakejiba, tausayin Galadima yakeji matuk'ar tik'ewa, Dan ganin rai kusan 15 kowa k'iyayyarsa akansa take da muguntarsa... ★★★★★★★★★★ Tunda Galadima ya shigo bai zaunaba, saida yagama had'a komai dazai buk'ata, yabama sarkin mota yakai cikin motar dazaiyi amfani da ita, alwala yay yafita salla massalacin masarautar, bai yarda sun had'u da Sarki ba, yay fitowarsa, koda ya dawo saiyasha magani ya kwanta, kaikace bashida wata matsalane, babu dad'ewa kuwa barci yay gaba dashi. Bai tashiba saida aka kira sallar la'asar, nanma massalacin yaje, bayan ya dawo yay kiran Momma ta video call, duk suna asibitin hardasu Samha, d'aya bayan d'aya ya gaisa da kowa, Samha harda kukanta tanason zuwa Nigeria, ita missing nasu takeyi sosai. Galadima yace a'a ba yanzu ba, tashi tai tabar gaban lap-top d'in tana kuka, Galadima ya girgiza kai kawai. Yasha hirarsa da Abie sosai, saboda Alhamdullah jikinsa saidai godiyar ALLAH, dama ciwo keshiga farat d'aya, sauk'i kam sai a hankaki. Addu'a kuma takobin muminice ako yaushe. Bayan ya gama waya dasu Momma Sir Isa ya kirashi, ya tabbatar masa da komaifa is done, Dan ansami kowanne acikinsu, yanzu haka wasu sunma iso. Galadima yay murmushi yana shafa fuskarsa. Yace, “Nama canja shawara, zamu canja gidan da zamu ajiyesu da, yanzu akwai wani gida annan kusada plaza d'ina, nagama magana da Saleem komai yayi ready, Ameer duk yakaisu can, insha ALLAH ana idar da sallar Isha'i zan fito”. Sir Isa yace, hakan yayi, dan acikin yaran nasuma za'a iya samun munafukai, tunda duk sunsan gidan daza'a ajiyesun, yanzu kuwa shi Ameer kad'ai zaisan da wannan. Galadima ya kira Munaya, dama tun d'azun kiran nashi take jira, ta d'aga tana shigewa cikin bayin d'akinsu Dan kar wani yaji. Galadima yace, “haryanzu kukan?”. “a'a” ta fad'a cikin share hawaye. Yad'an murmusa kawai yana fad'in, “Akwai bak'in da sukazo gidanku?”. “A'a babu Wanda yazo, sai Siyama da Zarah”. Galadima yay murmushin gefen baki yana cigaba da danna lap-top, hasashensa yazama gaskiya kenan, gyaran murya yad'anyi kad'an yana fad'in, “kina jina?”. Munaya tace, “eh”. “Ki saka ido akan d'akin Abba, motsin kowa yazama akan idonki koda cikin matansane, ko yayyenki maza, Dan za'a iya yin amfani da kowa, inda da dama ma key d'in d'akin yazama a hannunki”. Munaya tayi d'an jimm alamar tunani, zuwa can tace, “babu damuwa, zan gwada hakan insha ALLAH, amma kunji labarin Abban?”. “Karki damu, insha ALLAH Abba zai dawo gida, addu'a muke buk'ata”. Munaya ta jinjina masa kai tamkar tana ganinsa, ta share hawayenta dake zubowa. Yana yanke wayar nafito, cikin dabara nashiga d'akin innarmu, key d'in d'akin Abba Na d'akko, dukda nasan kowama yana dashi cikin matansa, fitowa nayi naje cikin dabara da sauri-sauri Na saka key d'in cikin k'ofa d'in, cikin addu'ar Neman nasarar kozai karye a ciki, amma ko gezo baiyiba, hannuna sai azabar zogi yake, danma nayi amfani da wani abin sarrafa k'arfene, cirewa nayi nakoma ciki kozan samo wani k'aramin k'arfe dazai iya Shiga, saida nasha wahala nanma sosai kafin Na samo, gashi duk a tsorace nake kar wani ya fahimci abinda nakeyi, cikin kafar makullin Na turashi, Alhmdllh nasamu ya shige, nagwada saka key amma yak'i Shiga, nasan babu yanda za'ayi wani key ya sake shiga wajen harsai mai gyara yazo, tunda kuma Abba bayanan ai babu buk'atar hakan, Dan duk wanda zai buk'aci shiga yanzu lallai akwai manufa. Dukda haka saida nasamo kwad'o nakuma sakawa sannan hankalina yad'an kwanta. ************************** *_9:00pm_* Fitowarsa kenan daga wanka baiko tsaya shafa mai ba ya hau shiri cikin wandon da riga k'ananu, fuskarnan babu alamar walwala tattare dashi, komai yana yinsane cikin karsashin fushi da damuwa, ya kammala tsaf yad'an saka turare. A k'ofar sashensa ya iske Nuren yana jiransa, sauran Hadeemansa dabasuyi barciba suka shiga masa barka da fitowa, kansa kawai ya d'aga musu, d'aya daga ciki ya bud'e masa bayan motar, amma sai bai shigaba ya d'aga masa hannu ya bud'e gaba da kansa ya Shiga, Nuren yay murmushi kawai, yasan yau mazan a wuya suke. Shiga yay shima mazaunin driver yaja suka fice. Gidane matsakaici sabo, dagani ko dad'ewa da gama gininsa ba'ayiba, saidai anzuba komai Na amfanin gida, ahaka suke buk'atar badashi haya. Dan haka da saleem yanemi hayar suka bashi kai tsaye. Suna isowa Muftahu ma ya iso d'auke da su Harun, Alhj Darma, Farhat d'iyar Minister sai mal. Saminu driver Alhaji balala, kusan shima yana hannunsu har yanzun. Ameer ya mik'e da Sauri yana salute d'in Galadima, hararsa yayi, Ameer yay murmushi yana yin k'asa da kansa. Cikin girmamawa yace, “Ranka ya dad'e wad'annan sune phones d'in yaran da tarkacen kayamsu”. Jinjina kai Galadima yayi, hannunsa duk biyu goye a bayansa yana zagaya table d'in da aka zube wayoyi, da lap-tops, iPad's dukna wad'anda aka kawo d'in, ya kalli Ameer cikeda k'asaitarnan tasa yace, “Suna INA?”. “Duk suna sama ranka ya dad'e, Dan inaga yakamata kazauna acan, danka ke ganin motsin kowa daga waje, dukda ansaka cctv a ko ina na wajen”. Galadima ya kad'a kai alamar gamsuwa da bayanin Ameer. Cikin takunsa na izza da lafiya ya nufi saman benen dake gidan, Muftahu da Nuren suka kalli Ameer cikin neman k'arin bayani, murmushi yamusu, yana tattare wayoyin yabi bayan Galadima dasu. A k'aramin falon k'asan ya iskeshi tsaye yanabin komai da kallo, Ameer yace, “ranka ya dad'e yazamuyi da wad'annan phones d'in nasu?”. Galadima yad'an ciza lips yana kallon Ameer, yace, “inasu Nuren d'in?”. “Suna k'asa”. Galadima baice komaiba, hakan da yayi ya saka Ameer fahimta su shigo kenan, saiya ajiye abin hannunsa ya sauka k'asan Dan kiransu. Saleem yafito daga wani d'aki ya taso k'eyar wani matashin Saurayi k'yak'yk'yawa, daka gansa kasan hutu yagama ratsashi, kallo d'aya Galadima yamasa ya d'auke kansa, Saleem yaja kujerar dining d'aya ya zaunar dashi, sannan yasaka igiyar daya d'auka ya d'auresa jikin kujerar, saurayin sai zaginsa yakeyi, amma Saleem ko kulashi baiyiba, saida yagama tsaf sannan ya kalli Galadima, wata alama yamasa da ido. Sai kawai naga Saleem ya d'auke saurayi da wani shegen mari, Wanda yasaka su Nuren dake shigowa jan birki suna kallon Saleem, bakin saurayi bai mutuba, Dan haka Saleem yakuma zuba masa wani har hancinsa Na fashewa, azaba ta sakashi kama bakinsa yay shiru yana huci da had'iye hawaye. Galadima ya ta6e baki yana d'age kafad'a. Alamar sudai suka sani. Haka Saleem yayta fiddosu d'aya bayan d'aya harsu 7, maza 5 mata 2, sai Farhat cikon ta takwas, amma su matan babu wacce aka d'aure, mazanma idan har bakayi gardama ba ba'a ta6asu. Saleem yagama jerasu reras gaban Galadima daya d'ora k'afa d'aya kan d'aya cikin kujera yana danna lap-top hankali kwance. Muftahu da Nuren dai sunyi mutuwar zaune, basu ta6a tunanin Galadima zaibi wannan hanyarba, gashi yak'i basu wata fuska dazasu masa magana ko tambaya. Saleem da Ameer suka kamo Harun shima aka d'aureshi a gefe ba cikin yaranba, shi baima cikin hayyacinsa, Dan su Nuren saida suka shak'a masa Abu, Alhj Darma da m. Saminu ne kawai ba'a d'aureba, suma dai aka kawosu gabansa aka zube. Galadima ya d'ago yana kallon su Muftahu dasuka Gaza barin kallonsa, cikin ta6e baki yace, “kallonfa?”. Ajiyar zuciya suka saki a tare, Nuren yace, “Brother mufa bamu fahimtaba”. Lips yad'an ciza yana ta6e baki da fad'in “Duk wannan dalla-dalla d'in da akai muku?”. Shiru sukayi Dan inhar a fahimtarsuce dai yau sunzama Kidnappers Na gaskiya kenan🤭😂. Galadima yace, “Well, Ku ajiye zancen fahimta gefe, kuduba phones d'in su Wanda babu charge a saka, Dan zuwa safiya duk za a fara aiki dasu, daganan mai buk'atar barci yaje ya kwanta kawai, sauran aiki sai safiyar gobe”. Babu Wanda ya iya cewa komai, dan sunsan dai Galadima bazai sakasu a had'ariba saboda son zuciya, Ameer ya fidda Chargers suka saka dukkan wayoyi ajikin caji, Dan akwai wuta. A wannan daren Galadima ya tura sak'o ga dukkan iyayen yaran, lokacin duk sunbar wajen Abba sun koma gida, anbarsa da garadan samarinnan akan sai washe gari, Dan sun tsarama su Zarah duk yanda zasuyi. Babbar magana, Alhaji Mansur habibu Uba yana shirin kwanciya barci wayarsa tayi tsuwar shigowar sak'o, sharewa yayi, hakan kuma saiya saka matarsa a zargi, tatashi zata d'auki wayar ya hana, saita kuma tsarguwa, a zarginta wata shegiyarce ta turo masa, ganin ta fusata saiya bud'e sak'on. Babu shiri ya dirgo daga gadon a tsorace yana tambayarta ina nerh-nerh take?. Da mamaki race, “batace ta sanar maka zataje wajen Rahma ta kwanaba?”. A rikice yace, “Rahmar ubanwa, maza kiramin ita yanzunnan su Abubakar suje su d'akkota”.. Bata fahimci inda ya dosaba, amma rikicewarsa saiya sakata d'aukar waya ta kira nerh-nerh d'iyarsu, wayar na Shiga amma ank'i d'agawa, cikin tsantsar tashin hankali ta sanar masa, ya daka mata tsawa yana fad'i “ki kira Rahma d'in ko wani d'an gidansu mana!!”. Maida akalar kiran tayi kan Rahma, itama dai ank'i a d'aga, bataso kiran Hajiya yalwa ba, dan atunaninta kota kwanta, amma dole ta kiratan. Hajiya yalwa Na zaune kusada mijinta Alhaji Abdul-Naseer Nafi'u kiran ya shigo, tayi mamakin Kiran, Dan hajia Marya bata kiranta a irin wannan time d'in, saitayi tunanin ko takasa hak'urine da rashin nerh-nerh abinka ga auta. Cikin raha tayi picking tana nunama mijinta wayar da baki, yay y'ar dariyarsu ta manya yana kuma kishingid'a da zubama matar tashi idanu. Tambayar da Hajiya Marya tama hajiya yalwa ce ta rikitata, ta mik'e zumbur tana fad'in “bara Na duba to, Dan wajen 3pm suncemin zasuje zaga gari, amma 7 zasu dawo gida, to wlhy bak'i mukayi suka d'auke hankalina nikuma ban nemi ganinsuba, tunda ina tunanin sundawo suna sashen Rahma”. Duk kiranda Alhaji Abdul-Naseer kema hajiya yalwa batajishiba, hakan ya sakashi biyota. Kusan atare suka iso sashen Rahma d'iyarsu, y'an aikinta guda biyu Na zaune a falonta sunata gyangyad'i, kai kace sashen wata mai aurene ba budurwa y'ar 17years ba, Dan itace autarsu suma. Hajiya yalwa ta dakama masu aikin tsawa tana tambayarsu ina su Rahma?. A rikice sukace suma dawowarta suke jira tun d'azun (Dan sunsan inhar ta iske sunyi barci zasu yabama aya zak'inta, maybe ma yazama sanadin barin aikinsu). Alhaji Abdul-Naseer yana k'ok'arin gwada kiran Rahma shima irin sak'on Alhaji Mansur ya shigo masa. Ai sai suka kuma rikicewa, Ashe sak'o dukya jema sauran abokansu, dan dannan suka Shiga kiran juna kowa yana tabbatarwa d'an uwansa Galadima ya d'auke masa d'a ko y'a. A wannan Daren suka sanarma police, gidajennan 11 babu Wanda ya rintsa barci, dukda yaran 8 ne a hannun Galadima, biyu basuda sauran yara a gabansu, duk sunyi aure, Galadima kuma yakafa musu nasu tarkon ne daban, biyu kuma a ciki bamasu ta6a haihuwa ba, biyar sun mutu yace bashida matsala da matacce, shi wannan saisunje babbar Court ALLAH zaimusu nasu hisabin. Sauran yaransu irinsu Alh halliru kuma yace nasu mai sauk'ine tunda manyansa suna hannunsa. Tun a wannan daren manyan police suka Shiga Neman ina Galadima yake, tunda kai tsaye yasaka sunansa a sak'on messages d'in daya turama iyayen yaran. Galadima yarigada ya tsara komai yanda ya dace, duk wata waya dazata fita a wayarsu saiya ganta yakumayi recoding d'in maganar, wannan yasa duk abinda suka fad'ama police yaji, murmushi kawai yaytayi, yayinda su Nuren sudai hankalinsu bai wani kwantaba, dukda sunji dad'in rikicewar da mak'iyar Galadima sukayi. Abinka ga manya, tun a labaran 12am Na daren ranar aka fara saka maganar, labari yafara shiga kunnuwan wad'anda basuyi barciba. Ciki kuwa harda y'an masarautar gagara badau. Hankalin mai martaba ya tashi, a Daren ya aika jakadiya data rako matarsa turakarsa kiran Galadima, danya kira wayarsa switch up. Lokacin da jakadiya taje sark'in k'ofa ya tabbatar mata Galadima ya fita tun farkon dare. Komawa jakadiya tayi ta sanarma mai martaba, aiko yakuma shiga tashin hankali, minene haka Sameer dayake kallo mai nutsuwa da hankali ya aikata?. Yana cikin wannan damuwa Waziri ya kirashi, ya tabbatarmasa Sameer ya turo masa sak'o shima Harun yana hannunsa. Zuface ta shiga jik'a mai martaba, yanzunan duk jajen da akeyi Na 6atan Harun d'an waziri dama Sameer yasani amma yay kunnen uwar shegu da kowa, hazbinallahu wa ni'imal wakil, shikam baya fata wannan mummunan labarin yaje kunnen 'Dan uwansa dake kwance cikin halin matsananciyar jiyya (kunsanfa har yanzu babu Wanda yasan samun sauk'i da Abie yakeyi, bayan ahalinsa dasu papi) a gagara badau babu Wanda yasani. Su Galadima duk suna ganin abinda ke faruwa a TV suma, amma ko'a kwalar rigarsa, damuwa d'aya kecin ransa halinda Abban Munaya ya tsinci kansa a ciki, amma sauran matsalolin dama dukya dad'e da shirya abinsa, komi zai biyo baya dama zuciyarsa ta shirya d'auka. Yau dai kam kusan a zaune suka kwana, abin tausayi saiga Galadima da kwannan kujera, aiko yasha wahala, Dan tashi yayi jikinsa Na matuk'ar masa ciwo, d'akin da aka saka masa kayansa yashiga, yasamu yay wanka sannan yayo alwala sukayi salla a jam'i, Dan har yaran duk kwancesu akayi, wad'anda kuma basayi suna zaune daga gefe. Galadima yace Ameer yaje da y'ammatan su had'a musu breakfast, cikin cika umarni yatasasu gaba suka fice, saidai kuma Farhat ce kawai ta iya girkin a cikinsu, gashi tanada Asthma, bakomai take iya sakewa wajen yiba, haka dai Ameer ya saka Nerh-nerh da Rahma suka taimaka mata da Abu mai sauk'i, dayake a tsorace suke, komai aka saka su yi sukeyi, sunga zuk'ek'iyar bindiga ahannun Ameer yo🤭😂. Koda aka kawo abincin dukda tashin k'amshi da yakeyi Galadima cayay bazai ciba, sudai su Muftahu kam ci sukayi, shikuwa yak'are dacin cake da tea, Wanda dama da kayayyakinsa yazo caf (Galadima fa da shirin zama yazo🤣 fans). Tun'a daren jiya gidan da su Galadima suke aka zagayeshi da y'an sanda, yasan kuma da hakan Dan CCTV Na nuna masa komai, amma saiyayi tamkar baima San da zuwansuba. Harun dai yak'i ci shima, hasalima sai yankama Galadima magana yake, wai inhar ya isa shid'in shegene ya kwanceshi mana, Ashe shid'in matsoracine ma, Dan ba'a sake d'aure kowaba bayan sunyi salla saishi Harun d'in daya nemi yin gardamar k'in nutsuwa waje d'aya. Ko inda yake Galadima bai kallaba. Nuren yay gyaran murya, duk suka maida attentions d'insu garesa. Yace, “inhar kun shirya bamu had'inkai kowa zai fita a gidannan lafiya babu ko kwarzane a jikinsa, Dan bamuda matsala daku, da iyayenku mukeyi, Wanda yaza6i kuma tafiya barzahu babu shiri saiya nuna jarumtarsa ko rashin kunya, wannan wawanma ya isheku izna”. Yay maganar yana nuna Harun daketa bige-bige yana kumfar baki masifa. Duk suka amsa da zasu bada had'inkai. Yau dai Darma kam shima yashiga hankalinsa, Dan yaga lamarin yafi k'arfinsa. Galadima ya d'auki k'aramar wata waya dake kusa dashi yafara dannawa yana shan tea d'insa hankali kwance, yayinda k'afarsa ke hard'e d'aya kan d'aya. Munaya ya kira, wadda itama batayi isashen barciba, gashi suna a yanayin rashin tsarki balle ta duk'ufa gayama ubangiji itama, amma dukda hakan bata fasaba, zuwa dare kuma kowa ya ankara da rashin dawowar Abba akwai matsala, dan around 7:30pm Baba k'arami ya dawo gida, babu dad'ewa kuma saiga Dady shima, dawowarsu yasaka kowa Sanin mi ake ciki, innaro ce kawai aka hana kowa ya sanar mata. Babu Wanda yay barcin kwanciyar hankali a gidan su Munaya, saidai yaran k'anana dabasu San dawan garinba, irinsu Inna ma ai akan sallaya suka kwana suna gayama ALLAH kukansu😭. Basuda wuta a daren jiya, shiyyasa basuga abinda yake faruwaba, rashin kwanciyar hankali ya hana a kunna musu gen..., Gasu Abdurraheem kwana sukayi kuka.🤦🏻‍♀ Cikin sanyin jiki Munaya ta d'aga kiran, muryarta ta dushe saboda kuka, ahaka ta gaisheshi. Ya amsa a sanyaye shima yana tambayar yaranshi, tace, barci sukeyi. Cikin lumshe ido yace, “karki damu daduk abinda zaki gani, sannan karki kirani, dan duk kiran dazakiyi nasan baizama lallai nikad'aine zan jishiba, zan dinga kiranki dakaina insha ALLAH. Please take care of yourself”. Kitt ya yanke wayar batare da yajira cewarta ba. Kanta ta cusa cikin k'afafu ta fashe da kuka, yayinda Munubiya ma ke gefenta tana nata da shayar da Ameen daya tashi barci. Galadima kuwa yana yanke wayar ya mik'e cikin takun izza da k'asaita ya k'arasa gaban Harun da bakinsa yakasa yin shiru. Izzarsa da k'asaitarsa Na burge matasan samarin nan, hakan yasa duk suka bishi da idanu har y'ammatan, ga fuska a cakud'e babu alamar yasan minenema dariya. Gaban Harun ya tsaya hannayensa duka a cikin aljihun wandonsa, babu Wanda yakula da lokacinda Galadima yaciro hannunsa d'aya a aljihu, saidai k'arar mazgar Harun dayayi abaki sukaji kawai, kafin Harun ya farfad'o Galadima yakuma k'ara masa ta d'ayan gefen. Sannan ya d'an risuno yanama bakinsa alamar zip da yatsunsa biyu🤐, Harun yamasa shiru kenan🤣. Kutt, gaskiyafa Harun ya mazgu babu k'arya🤭🤣. Amma d'an bala'in naku bakinsa bai mutuba, bayan ya farfad'o daga azabar dukan saiya cigaba da magana cikin haki da huci. Sharesa Galadima yayi yakoma ya zauna dan fuskantar abinda ke a gabansa, a fusace ya d'auki k'aramar bindigar daya fiddo yanzu yafara Harbin inda Harun yake, ta saitin k'afafunsa. Rikicewa kowa yayi, Harun yashiga mutsu-mutsu da k'afafu yanasan d'agewa Dan kar Harbin ya sameshi. K'aramin d'an iska Ashe kanajin tsoron mutuwa🤣?. Wannan harbi ya kid'ima police d'in dake a wajen gidan, akuma dai-dai lokacinne manyansu suna iso suma, kuma duk sunji harbin.............✍🏻 Humm babbar magana, komiye shirin Galadima Na zama kidnapper?.🤦🏻‍♀ Wane ahiri kuma su Zarah sukazo dashi gida🙆🏽?. Sannan wane shiri Galadima yake akan ku6tar Abba? tunda yace plan B😔☹. Ina baba mai kanwa? Wane taimako zaibamu shima😭. Kumuje zuwa my guys karku k'osa dai, sannu-sannu bata han[8/3, 3:35 PM] +234 810 341 4063: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣6⃣ .................Jin tsayuwar motoci ya saka Ameer lek'awa ta window, juyowa yay ya kalli Galadima, “Ranka ya dad'e y'an sandane”. Baki Galadima ya ta6e, ya share tamkarma baijiba, yana cigaba da bud'e wasu file daya fiddo a briefcase. Saida yaja kusan 1 minute sannan ya mik'ama Nuren dake kusa dashi wasu files, ya zaro takarda kuma yay rubutun dabai Gaza layi biyarba ya mik'ama Ameer da wata k'amar waya a kwali. Kar6a Ameer yazo yayi, batareda Galadima yayi magana ba ya nuna masa window. Muftahu daya fahimta yace, “Ameer ka jefa musu takardan da wayan”. Ameer ya amsa da to, yanufi window d'in, cikin dabara ya jefa kwalin da takardar. Wani d'ansanda dayaga tahowarsu yay saurin zuwa kusada window d'in, ALLAH yabashi nasarar cafewa. D.p.o dake tsaye tare da sauran police ana shawarar yanda za'a shiga gidan ya kaimawa. Yay salute nasu kafin ya Isar da sak'on dukda yasan duk sunga daga ina kayan suka fito, d.p.o ya gyara tsayuwarsa yana fad'in “bud'e kwalin mu gani”. Bud'ewa yayi, yaciro wayar yana cewa, “wayace sir”. Cikin ta6e baki d.p.o ya jinjina kansa, yace, “takardar fa?”. Itama bud'ewa yayi, yafara karanto abinda ke jiki, wanda Galadima ya rubuta da harshen nasara. *_Kamar yanda suka fad'a Muhammad Sameer ba d'an ta'adda baneba, inhar zakubi yanda nace lallai yarannan zasu fita lafiya, idan kuma har kuka nuna k'arfin iko, zanta jeho muku gawarsu d'aya bayan d'aya ta saman benenan, ga wayanan, idan kuna buk'atar magana koni ina buk'ata ta wadatar, Dan kar wani yay gigin cewa zai shigo. Idan nayi ba dai-daiba a gafarceni👏🏻_* Daga d.p.o har jama'ar dake kusa dashi duk ajiyar zuciya suka sauke, ya jinjina kai yana cije bakin mamaki, cikin sauke numfashi yace, “saimu bishi yanda yakeso mugani, idan munga zai mana wasa da hankali sai a d'auki mataki, C.. babangida a zagaye gidan”. “Ok sir”. C babangida ya amsa yana salute nashi. Dandanan suka warware wani blue d'in zare suka zagaye gidan dashi, mutanen anguwa dasuka fara fahimta harsun fara taruwa kallo, harma wad'anda sukaji a labaran sunfara gangarowa anguwar damin ganema idonsu. Duk abinda ke faruwa Galadima Na zaune k'afa d'aya kan d'aya yana kallo ta CCTV, sai famar buga pen yake saman la66ansa a hankali, suma dai su Muftahu dasu Harun suna kallon komai. Kujera aka kawoma d.p.o ya zauna, dayake da sauran safiya babu maganar neman runfa ko umbrella. Wayar d.p.o ya kar6a da kansa, dan case ne Na manya IG da kansa yakirashi, yakuma abbatar masa shima yana nan zuwa. Shiru d.p.o yay yana bincikar wayar da Galadima ya aiko da ita, babu komai a cikinta sai Number guda d'aya, baice komaiba yaciro wayarsa yayma IG bayanin komai. Daga can IG yafara fad'a, wai tayaya zasu saurareshi, bayan d'an ta addane, duk Wanda zai iya kidnapping aiko d'an ta'addane, kawai su nuna masa k'arfin iko wajen ku6tar da yaran. Shidai d.p.o ya kwantar da murya cikin sigar lallashi yace, “Nidai Sir da ace za'abi ta tawa daminbishi a hankali, maybe akwai sak'on da yakeson isarwa, karfa mu manta shima d'an manyan mutanene, shikansa akwai sarauta mai daraja a kansa, ai mai martaba bazai ta6a jin dad'iba shima, tunda ya buk'aci dama mu bashi, idan munga batai manaba saimu d'auki mataki”. IG yace, “shikenan, Ku kirashi muji miyake buk'ata, nima a had'a dukkan maganar da zakuyi dani naji komai, dukda munama hanyar isowa yanzunan”. Cikeda farin ciki d.p.o yace, “ok sir”. Duk kayan aikin dasuke buk'ata suma sun tanadesu, yayinda y'an jarida suka fara isowa wajen. Shima C.P ma saigashi ya iso, duk suka k'ame wajen salute nashi har d.p.o. Ya amsa musu cikin jinjina kai, sannan ya buk'aci jin mi'ake ciki?. Bayani d.p.o d'in yamasa, shima ya gamsu da shawarar abi komai a sannu d'in. Galadima ya murmusa yana lumshe idanunsa yana sauke ajiyar zuciya. Saboda dukkan wayar da d.p.o yay da IG a kunensa ne. Sudai su Nuren sunyi jugum-jugum Dan son ganin minene shirin Galadima waine?, da har yaza6i fiddo kansa wa duniya a matsayin mai laifi?. Kiran da C.P yayi da kansane ya shigo wayar Galadima bud'e ido yayi yana kallon su ta CCTV, sannan yay picking call d'in, shiru yay yak'i magana, saida C.P ya fara masa sallama sannan ya amsa. C.P yace, “Ranka ya dad'e barka da safiya”. Baki Galadima ya ta6e, ya amsa da “Barka dai”. Gyara zama C.P yay yana kallon saman gidan, duk su Galadima suna ganinsa, yace, “Ranka ya dad'e muna saurarenka, ka fad'i buk'atar taka, inhar batafi k'arfinmu ba za'a biya maka insha ALLAH ”. “Humm” Galadima ya fad'a yana mik'ewa tsaye, duka hannunsa Na zube cikin aljihu, dayake yana amsa call d'in ne da abin da ke kunnen sa. Falon ya shiga zagayewa cikin takunnan nasa na k'asaita da izza, saikace namijin tantabara yana gwada gasar tafiya a gaban matarsa😜🤣. Suko sai binsa da kallo suke tamkar wani magiji. A hankali yace, “Buk'atata ta farko shine iyayen yarannan su fiddo Alhaji Auwal fharuk, idan sunyi haka lallai zakuji manufata kai tsaye batare dana ja muku raiba, Dan nima ina buk'atar hutu”. C.P ya shiga jinjina kansa kawai yana sauraren Galadima da dukkan sauran police d'in dasuma sukeda alhakin jin komai ta hanyar abinda suka saka a kunne. Bai k'ara komaiba ya yanke wayar, Yakoma mazauninsa ya zauna yana kallon yaran dasuma dukshi suke kallo, d'an murmusawa yayi yana d'aukar ruwan daya ajiye, saida ya bud'e murfin ya mik'ama Wanda yake kusa dashi. Shima yay murmushi yana girgiza kai da fad'in “A'a ranka ya dad'e, Na gode”. Galadima ya mik'ama sauran suma, amma duk sai sukace A'a, murmushi yayi yasaka kayansa a Baki yasha, yana kallon Harun daya zuba masa ido, rabi yasha ya mik'ama Harun sauran, amma saiya kauda kansa gefe, Galadima ya ta6e baki yana d'aga kafad'a alamar kaika Sani. Sauran ruwan ya ajiye yana kuma kallon yaran, da hannu yakuma yima Na farko alamar yaya sunansa?. Bai fahimtaba Dan haka ya kalli Na kusa dashi, sannan yakuma kallon Galadima yana nuna kansa da fad'in “Sunana wai?”. Galadima ya jinjina kai yana lumshe idanu. “Sunana Ahmad Bana bb gana". Galadima ya had'e yatsansa babba da manuniya👌🏻 alamar nice name. Ahmad yace, “Thanks you sir”. Na kusa dashi Galadima ya sake nunawa, shikuma yace, “Ahakam Balala”. Shima jinjina Galadima ya masa, nakusa dashi kuma Gebirel Timothy, sai Nerh-nerh Bilkisu Mansur, Rahma Abdul-naseer, Yassar Mamman, Sulaiman sager sulaiman, Marcel Miracle. Cikin murmushi Galadima yace, “Duk sunan y'an gayune daku”. Gaba d'aya suka sanya dariya, banda Harun da Alhaji Darma, Harun yasan Galadima sosai, dama yanada tsokana idan yaso hakan, koda kai zakayi dariyar shi ya fuske kuwa. Galadima Yakuma fad'in “Duk kun kammala Secondary schools ne?”. Duk suka amsa da eh, kowa yashiga fad'a masa matsayin karatunsa da abinda suke karanta, dukda ba magana yakeba murmushinsa Na sakasu farin ciki..... .............★ A can kuwa waje, police nata k'ullawa da kwancewa da jiran isowar IG, Dan yace su jirayi zuwansa. Dukda Galadima yana hira da yaran hankalinsa nakan saurarensu ta abinda ke kunnensa. Babu dad'ewa saiga IG ya iso, kar6ar wayar yayi da kansa bayan sungama salute nashi ya zauna, ya kuma kiran Galadima da kansa. Galadima yay picking amma sai yak'i magana yanzunma, hakanne yasaka IG yin magana cikin takaici da fusata, “Kai bamason rainin hankali, kafad'i abinda kawai kakeso duka amaka kabasu yaransu”. K'ala Galadima bai ceba ya yanke wayar. Mamaki ya kama IG, C.P yace, “Sir dadai anyi hak'uri an musu magana kawai suma aji mizasu ce”. Cikin matuk'ar takaici IG ya dangwarar da wayar yana huci da cire hular kansa, da hannu yayma C.P umarnin a kirasun. Da Sauri Aka danna kiran wayar d'aya daga cikin su, dama duksun tattarune a waje d'aya, Dan haka ya saka Hans free duk sunaji. C.P da kansa ya sanar musu buk'atar Galadima, kallon kallo aka dungayi, kowa ya kasa magana, Shidai C.P ya yanke wayar yana fad'in “nanda mintuna 10 zasu kira”. Suna ganin C.P ya yanke wayar suka hau cecekuce da fad'in yaronan yagama raina musu hankali, kaza-kaza dai, wasu suna bada goyon bayan abadashi sai abi tawata hanyar a kar6i camera d'in saboda suna matuk'ar k'aunar yaransu, wasu kuma sunce kar'a sakeshi, Dan haka tamkar tonon sililine agaresu. Sundai kasa samun matsaya har 10minute's ta cika C.P ya sake kira. Ba'a samu Wanda ya iya d'agawaba harta yanke....... (**************************) Zuwa yanzu gidan su Munaya sunsan halin da'ake ciki game da Galadima dakuma maganar fitowar Abba, Dan y'an jarida nata yad'a komai live a gidajen redio da TV, ga masu d'auka a waya y'an gani da ido dasukazo suka kafa suka kuma tsare. Kuka dai Munaya Na shansa, tayi wujigi-wujigi, miji da Uba duk suna cikin matsala, da k'yar inna ta bata tea tasha da kanta, yaranma sai an mata dole take shayar dasu, ta lafe jikin innarsu tanata hawaye daga ita har Munubiya, yaran sai innaro dasu mama rabi'a da sukazo gidan Tun farar safiya ke kula dasu. A can gefe kuma Zarah da Siyama NATA zagayen d'akin Abba Dan son samun damar shigewa su d'auki camera🤦🏻‍♀. ************************** Alhaji Hallurune yabasu shawarar su d'auka kawai suce su k'arya ake musu Alhaji Auwal baya hannunsu. Wannan shawarar sukabi, da Kansu suka kira C.P suka shaida masa. Sharri Galadima ke musu. Galadima dakejin komai yayi murmushi kawai yana cizar lips. Laptop d'insa ya janyo yafara danne-danne. Daga can C.P ya yanke wayar yana Neman izinin IG domin kiran Galadima shima. IG ya bada izini zuciyarsa Na sakejin zafin Galadima da rainin wayonsa. Saida ta kusa tsinkewa sannan Galadima yay picking, C.P ya sanar dashi amsar da suka bada. Cikin murmushi mai sauti da har su C.P sukeji Galadima yace, “ga za6i biyunan, kodai su fad'i inda yake, kokuma su sakoshi, kokuma shi yasaki video d'in yanda suka saceshi”. Jikin C.P fa kansa yafara sanyi, Dan yafara hango k'amshin gaskiyar Galadima. Bindiga Galadima ya nuna Alhaji Darma da ita, yamasa alamar ya matso gabansa, jikin Alhaji Darma Na rawa ya matso, waya ya mik'a masa, sannan ya danna kiran su C.P yana fad'in a had'ashi dasu yanzunan. Kallon IG C.P yayi, alamar neman izini, IG ya bada damar hakan. Dan danan aka had'a Galadima da su, bindigar hannunsa ya d'ora saman kan Ahmad, maimakon Alhaji Darma, jikin Ahmad yafara rawa, tuni yafara kuka saboda tsoro, tsawa Suka dakama Galadima daga can. Ahmad daketa mazari ya sanya kuka yana fad'in “Dady please and please kubashi abinda yakeso Dan ALLAH, wlhy zai kasheni, wayyo daddy I love you so much”. Tuni Alhaji Bana ya rikice jin muryar d'ansa, Galadima ya cire bindigar daga kan Ahmad ya harbata gefe, k'arar ta tsorata su Ahamad suka rikice da ihu. Rud'ewa su Alhaji Bana sukayi, Dan azatonsu Galadima ya kashe Ahmad ne, su kansa su IG dake waje duk sun tsorata da tunanin ko Galadima ya harbi wanine a cikinsu. Galadima yace, “idan Baku shirya sakinshiba zan kashe Na gaba kuma”. A tare suka hau ihu kowa yana rige-rigen fad'in zasu saki Abba. Galadima ya ta6e baki yana gimtse kiran. Alhaji Bana dai ya suma tuni, saboda tunanin an kashe masa d'a. Saidai suka zuba masa ruwa ya farfad'o, kuka rurus yashiga musu yana kiran sunan Ahmad d'insa, Yakuma rikicewa lokacinda Hajiya Fannah Maman Ahmad ta kirashi. Kasa d'agawa yayi....... **** Galadima yay kiran su IG yana fad'in “inhar suka nakasa Abba ko kawoshi da wani mummunan raune abakin ran d'aya daga cikin y'ay'ansu, Dan haka a matsayinsu Na police su gargad'esu. ********* Antura Police inda suka kwatanta aje a d'akko Abbansu Munaya. A inda aka d'aukeshi suka iskeshi ajiye cikin mota a sume, haka suka d'akkoshi suka taho, kai tsaye asibiti aka wuce dashi domin duba lafiyarsa, dukda babu wani ciwo a jikinsa Na alamar duka sai fashewar baki da kumburin da fuskarta tayi shima bada wani yawa can sosaiba. Galadima sunga komai a TV saboda nunawar da akeyi, hawayen da suka taho masa ya had'iye da k'yar yana sunkuyar dakai danma kar wani cikin yaran kosu Muftahu su fahimci wani Abu, saidai tuni Nuren and Muftahu da Harun sun fahimceshi, Dan sunsa halayyarsa duka, yana da tausayi ainun. Ran Harun A 6ace yake akan bada Abba dasu Alhaji Mansur sukayi, zuciyarsa sai tafarfasa takeyi, gashi kuma a d'aure. Galadima ya mik'e yana bada izinin kowa yaje yay alwala time d'in salla yayi. Idan kuma anyi salla su Farhat su shiga kitchen nema musu abinci. Wannan adalci Na Galadima yanata tasiri a zukatan yaran, harsu gebiral. Duk yanda Galadima yace haka sukayi, har Harun dake d'aure saida aka kwanceshi bisa tsayawar Ameer kansa da bindiga yay alwala. Koda su IG suka nemi yin magana da Galadima saiya jefa musu takardar yana sanar musu time d'in salla yayi, bazai sake saurarensuba sai yayi salla.. Dole sukabi yanda yakeso, suma kuma ya tunatar dasu abinda suka manta. .............................★ Bayan idar da salla da gama girkin su Farhat aka kawo abincin kowa ya d'ebi iya buk'atarsa, yanzuma Galadima bai Ciba, kwanciyarsama yayi cikin kujera ya lumshe ido. Harun dai anji wahala anci yanzu🤣😜. .............................★ Tuni mazan gidan su Munaya suka d'unguma zuwa asibitin Dan duba halin da Abba yake ciki, matan dai da yaran an barsu a gida, sai innaro kawai data Dage sai taje aka tafi da ita. .............................★ Buk'ata ta biyu da Galadima ya kawo bayan idar da salla itace a tura jami'an tsaro suje subama iyalan Abba tsaro a gidansa, hakama a asibiti. Babu musu IG yasaka C.P, shikuma CP yabama D.P.O Umarni, dandanan aka sanar da station d'in yankin su Munaya, aka kuma k'ara dawasu police d'in harda mata da zasu shiga cikin gida. Munaya taji dad'in hakan da Galadima yayi, Dan a tsorace tale dama. Dole kuma Zarah da Siyama suka nutsu, Dan Munaya k'ofar Abba taja zugar y'an uwanta suka shimfid'a tabarma sukayi zaman jugum-jugum d'in a can.🤨👍🏻. ************************ A masarautar gagara badau kam babu abinda kakeji Na tashi sai k'ananun magana. Bayi da kuyangi, dogarai da y'an gidan, manya da yara, kowane hadimi burinsa yafara kaima sashen dayake gulma, sunyi gungu-gungu suna tayi, sai anga wani babba zai wuce saikiga an watse. Mai martaba ya kira papi, dukda yasan shima yaga komai, bayan sun gaisa a mutunce irin gaisuwar d'a da uba, suka shiga tattauna abinda ke faruwa, papi yace, ya kirashi amma wayarsa a kashe, yakira Nuren ma shima waya a kashe, Dan yasan lallai a tare suke shuka wannan tsiyar. Mai martaba yace, “To amma Abba kaga kuma yanzu ga surukin namu sun fiddo kamar yanda ya buk'ata. Ina ganin akwai wani Abu da Sameer keson ankarar da jama'a Wanda mu bamu San dashiba, nasan halin yaronnan yanada k'yawawan halaye ababen koyi......”. Cikeda 6acin rai papi ya katse mai martaba, “Jalaludden komai k'yawun halin Muhammad a yanzu ba kowane zai gansu koya yarda dasuba, dukda inaji ajikina bawai ganganci ya sakashi yin hakanba, dama yanada hujja, amma miyakai Na kisa?, a labarai sun nuna ya kashe yaron Alhaji Bana, shin wannan halin mutanen kwaraine? Wannan hanyar dayabi fa bazata ta6a 6ullewa da shiba sai 6ata masa suna damu kanmu, daga fitowar maganarnan zuwa yanzu nasamu kira babu adadi”. Mai martaba yace, “kayi hak'uri Abba. Insha ALLAH zan shirya naje wajen zuwa anjima kad'an”. “Shikenan. Idan naga nima abin yayi tsamari zan taho”. Sallama sukayi kowa yana jimami akan lamarin. Tunda labari yakaima mama Fulani tashiga tafa hannu tana sallallami da fad'in “A lallai zai iya zai aika, yo wannan yaron mai ido a tsakar goshi, fitinanne zai 6atama masarautarmu suna akan wani banzan talakan surukinsa, akuwa yanda ya kashe d'an mutane shima kasheshi za'ayi, idan munan ya rainamu yanzu kam ya d'ebo ruwan dafa kansa, fand'ararre kawai gagararre”. Haka taita k'ananan magana da jifan Galadima da munana. Oho shi baimasan tanayiba☹😏. ******************** A asibiti likitoci sun Shiga bama Abba taimakon gaggawa, Dan ba'asan minene ya sumar da shiba, tunda babu wani alamar duka ko harbi ko makamancin wannan a jikinsa.. ************** Suma police sun buk'aci Galadima ya basu gawar Ahmad. Murmushi yay yana kallon Ahmad d'in dake zaune yana shan ruwa saboda tsoratar dayayi sosai ta harbin da Galadima yayi, har yanzu yakasa sakin jikinsa, salla ma da sukayi a d'arare yayita, yazata da gaske shid'in aka harba, saida Galadima yayma Saleem nunin abashi ruwa, Saleem yakawo ma Ahmad ruwa, a lokacinne ya farga da Ashe yanada rai bai mutuba🤣😜. Ya kar6i ruwa kuwa jiki Na rawa ya shiga kwankwad'a idonsa akan Galadima dake masa murmushi, yana bama su IG amsa da fad'in “karku damu yalla6ai. Inada freight d'in dazan dunga saka gawarsu anan, bayan aiki ya kammala saisu d'auki y'ay'ansu sumusu sutura, idan kuma sunyi abinda nakeso kaga magana ta k'are, gawar Ahmad kawai ce a k'asa dai yanzun, sai idan ank'imin yanda nakesone za'a samu fiye da hakan dai”. C.P ya jinjina kai yana gyara tsayuwa, idonsa nakan ginin, yace, “to miye buk'atarka ta gaba yanzu?, tunda gashi an maka ta farko ai”. “Eh tabbas anmin, dukda dai ankawoshi ba'yanda Na soba”. “amma ranka ya dad'e suma ai ankashe musu yaro d'aya”. Gira Galadima ya shafa da d'an yatsa yana ta6e baki, “ito dakuma wannan Dan wannan fa, yanzu dai inaga buk'atata tagaba shine ku kama mutanen nan guda 11 dazan lissafo”. “Muna saurarenka, dawa-dawa?”. Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, cikin Nisawa ya gyara zamansa yana d'aukar takardar dake gabansa ya shiga lissafosu. “Alhaji Balala, Alhaji Bana baba gana, Alhaji Abdul-Naseer Nafi'u, William Solomon, Hajiya A'i Barnawa, Alhaji Sageer Sulaima Sulaiman, madam Victoria, Mansur Habibu Abu, Josaya bamma, Alhaji Mamman k'afur, Alhaji Halliru garba”. Kallon kallo aka tsayayi tsakanin IG da sauran police, sai C.P ne yasamu k'arfin halin cewa “amma to Ranka ya dad'e akan wane dalili? Kasan dai bazai yuwu muje kama mutane babu dalilin komai damuka saniba”. Wani muskilin murmushi Galadima yayi, ya kwantar da kansa jikin kujera yana lumshe ido da cije lips, “Dalilin ai a fili yake yalla6ai namu, bisa dalilin Samun Alhaji Auwal Fharuk a hannunsu mana, dan yakamata asan dalilin samunshi a hannunsu, miya musu? Mi suke nema a wajensa? Baniba nasan dukan jama'ar garima abinda sukeson ji kenan, kunsan dai bazan ajiye ayukan gabana da jiyyar mahaifina nazo Nigeria Na zauna Ina kama yaran mutane saboda rashin aikinyiba ai, aimin kokuma nakuma aika yaronsu biyu barzahu yanzunnan!!”. Galadima ya k'are maganar cikin tsawa da matsanancin fushi. Tsawarsa saida ta kad'a hanjin yaran, hatta da Harun dasu Muftahu saida suka rumtse ido, suma haka police d'in dake sauraren Galadima. IG ya mik'e daga zaunen dayake yashiga safa da marwa Na mamakin wannan lamari, sukan ai ansakasu a tsaka mai wuya, cikin tsakkiyar fad'an manya. C.P ya kira suka koma gefe suna tattaunawa. ............................★ A can kuwa hankalin su Alhaji Sageer ya kuma k'ololuwar tashi, Alhaji Mamman yace, “lallai yaronnan anyi tsinanne, dama wannan ranar Na ringa gudu tun boss nada rai (tanderu yake nufi), amma wasunmu sukace yaron bai Isa mana komaiba, gashinan rana tsaka yana Neman zame mana RAINA KAMA....” “Yama zama ai, Dan gayya kawai muka fara gani yanzun”. ‘Hajia A'i ta fad'a a tsorace’. Duk sun kasa zama waje d'aya, Miracle yace, “yanzu nan da mutuncinmu za'ace wai y'an sanda su kamamu a k'asarnan?, lallai yaronnan yataro March wlhy”. “Kokuma mune muka taro March d'inba”. Alhaji Bana dayake cikin kukan mutuwar d'ansa yafad'a yana share hawayen. ...............................★ IG sun yanke shwarar bin umarnin Galadima kawai, kodan tseratar da yaran, yad'anyi magana da manyan dake kusa dashi dukda shine Oga kwata-kwata, kowadai yabada goyon bayan a kamasun kawai. Dan haka IG da kansa yay kiransu, Yakuma basu dama a girmamame akan sukai Kansu kawai station d'in dake kusa dasu, kodan rayukan yaransu, daga baya za'asan abunyi insha ALLAH”. Galadima dake saurarensu a zuciyarsa yace, abinyi kuma ai saidai a prison. Duk sunk'i amincewa, wasunsuma sai bak'ak'en magana suke fad'a. waya Galadima ya jawo yana daddannawa, sannan yayma Marcel nuni yazo, Dan yaji babansa yafi kowa zak'ewa, jikin Marcel sai 6ari yakeyi, ahaka ya rarrafo gaban Galadima. Galadima yace, “'Dauka wayarka anan”. Jikin Marcel na rawa ya d'auka. “Kira daddynka”. Dandanan yay kiransa, bugu d'aya kuwa ya d'auka shima jiki yana 6ari, duk suma sukayi tsitt suna jiran mizaice. Galadima ya d'orama Marcel binduga a tsakkiyar kai, ya juya idanunsa alamar yay magana. Marcel ya sanya kuka saboda tsoro. Rikicewa daddynsa yayi yana tambayar mi aka masa? Badai yay musu komaiba ba ko?..... Katseshi Galadima yayi da fad'in “Zandai yimasa, Dan kaima yanzu d'anka zai wuce Inda Na Alhaji Bana yatafi”. “kai kai dakata please ka dakata, nidai Na yarda zan mik'a wuya, karka ta6amin yaro kaji Na rok'eka”. Cire bindigar Galadima yay yana maida kunamar da fad'in “shawara mai k'yau, lallai kanason d'ankan nan, ka tambayi abokanka, Wanda bazai mik'a wuyanba saiya fad'a yanzun nan”. “karka ta6a mana yara please, duk zamu mik'a wuya”. Galadima ya tuntsire da dariyar da wanima zai iya rantsewa bai ta6a ganin yayiba, yace, OK, good dattijan k'asa, saina jiku acan”. 🤣🤣ana shagali a Nigeria yau kam🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀ amma Nigeria novel ba tamuba😜. Su Alhaji balala dai kam sun mik'a wuya, da Kansu suka kai Kansu police station mafi kusa, daga can suma d'aukesu zuwa inda IG yace. Galadima yay hamdala ga ubangiji dukda bawai komai yagama kammaluwa bane, amma lallai an d'akko hanya. Ya bada Umarnin tashi suyi sallar La'asar, kafin a dawo a cigaba da gashi😜. ....................................★ Bayan sun idar da salla C.P ya kira Galadima, suka shaida masa su Alhaji Bana suna hannunsu yanzu haka. Galadima dake tsaye yace, “Alhmdllh, zuwa safiyar gobe kuma sai a kai case d'inmu Court, Dan inason komai yafarune cikin gaggawa ya k'are, bana son jan jiki a aiki”. C.P ya kalli IG Dan jiran amsa. Kai IG ya jinjina masa alamar za'ayi hakan. C.P ya shaidama Galadima amsar IG. Galadima yace, shikenan, shi yatashi daga aiki, saikuma safiyar gobe. C.P zaiyi magana I.G ya dakatar dashi alamar ya barsa kawai. Ta6e baki Galadima yayi yana yanke wayar, ya maida kallonsa gasu Muftahu da duk suna maidashi television, gira d'aya ya d'age musu, sukuma sukai masa jinjina👍🏻. Kauda idonsa yayi ya maida ga yaran, yace, “yaya akwai mai buk'atar wanka ko barci?”. Gaba d'aya suka amsa da duk suna buk'ata. Kallon Ameer da Saleem yayi yabada Umarni da ido. ..............................★ 'D'aya bayan d'aya suka dinga kaisu suna wanka, duk Wanda yagama sai abashi lemo, batare daya San miye acikiba saiya shanye, daga sha ko mintuna 3 basa k'arawa suke 6ingirewa barci🤣. 🤣🤣ho Galadiman mu kasan takan tsiya, Zuma kenan, ga zak'i ga harbi🤸🏻‍♀, kaga Na Munaya baban triplets, bada kanka a sare kaje gida kacema su mama Fulani an k'illesa👌🏻😜😂. Da akazo kan Harun k'in tankawa yayi, Dan haka Galadima yace su barshi kawai, amma harsu Malam Saminu da Alhaji Darma su Farhat duk sunma Kansu gyad'ar dogo sunje sun mik'e zasu huta. Nuren ya kalli Galadima cike da tausayi yace, “Brother kaima kad'anje ka huta mana”. Murmushin gefen baki Galadima yayi, yajawo lap-top gabansa yana girgizama Nuren kai alamar a'a.................✍🏻 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu_*😭👏🏻 [8/3, 3:38 PM] +234 813 221 4515: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ___________________ *_Na gaisheku, gaisuwa irinta musamman d'innan. Makaranta buk d'in RAINA KAMA dake JAMI'AR KUST dake WUDIL, alkairin ALLAH yakai agareku, ALLAH ya yalwataku da ilimi mai tarin albarka damu baki d'aya._* Ina inyinku irin Trillion's d'innan my guys🤸🏻‍♀😘😘😘😘❤❤. ____________________ *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣7⃣ ...................Abin surutu lallai ya samu, mak'iyan Galadima kuwa duk sun kasance a tsorace, Dan ba kowane ya fahimci inda shirinsa ya dosaba, hakama a cikin masoyan nasa, wasu suna ganin daidainsa wasu kuskurensa, kowa da irin fahimtar dai da yayma lamarin. Yauma dai haka suka kwana zagaye da police. Amma su IG duk sun tafi, d.p.o ne kawai tare da tawagarsa, kamar kuma yanda ya buk'ata sunakan tattara case d'in zuwa Court. 6angaren su Baffi kuwa lauyan Abie dukkan shirye-shiryen shiga Court suma suna akanyi. Dan dukkan shirin Galadima yasan dashi tsaf, hakan yasa koda yagani baiyi mamakiba, kisan Ahmad daine da akace yayi yabashi mamaki, dukda zuciyarsa bata aminta Galadima zai iya kashe yaro ko d'ayaba. Amma lallai hakan ya sakashi a rud'ani, harma ya kira sir Isa sukayi maganar. Sir Isa yace shima yagani a labarai amma gaskiya bai yardaba, akwai dai abinda duk basu saniba, Dan Galadima bazai aikata hakanba. Da wannan maganar ne Baffi yad'an samu Nutsuwa yacigaba da tattara bayannsa daduk abinda zasu kafa hujja dashi a court. Duk abinda ke faruwa Momma tasan komai. Dan Galadima ya sanar mata, baya kuma 6oye mata dukkan shirinsa akan wannan case d'in dama, amma sai tayi lup tamkar batasan anaiba, koda labari yazo musu saita taya su Aunty Mimi rud'ewar itama, harda pretending d'in kukanta tana Neman number Galadima, amma sai tak'i wucewa. Daga Baffi har mai martaba babu Wanda ya kirata akan batun, duk a nufinsu Na 6oyemata kar hankalinta ya tashi balle Na mahaifinsa dake kwance yana fama da kansa. Amma saiga kira daga mama Fulani, tafad'ama Momma maganar daduk yazo bakinta ta 6atanci akan Galadima, itadai momma cikanki batace da itaba, har tayi ta gama ta yanke wayar. Saiga gimbiya Zulfah ma ta kira Momma, itakam ai harda kukan makirci irinna y'an duniya. Itama dai tayi kid'anta tayi rawarta Momma Na saurarenta. Koda ta Yanke wayar saita kira munaya. Taita kwantar mata da hankali da lallashinta akan ta kwantar da hankalinta. Insha ALLAH komai zaizo k'arshe, kowace rayuwa takan tafine da jarabawa. Babu wani rai dazai rayu cikin farinciki da samun yanda yakeso 100%, dolene kowacce rayuwa akwai NATA k'alubale, nakowa kuma akwai ta hanyar dayake fuskantar nashi. Sosai Munaya ta gamsu da nasihar momma hakannema yad'an samu mata nutsuwa tad'an rintsa a wannan dare. .................................★ *_WASHE GARI_* Nasara ta farko da aka wayi GARI da ita shine farfad'owar Abba cikin hankalinsa, saidai har lokacin baya sanin Wanda yake a tare dashi, hakanne yasaka likitocin fad'in a k'ara masa lokaci yasamu isashen hutu. Ahalinsa sunsamu Kansu a farinciki ainun, hakama masoyansa, shikansa Galadima Yakuma samun kwarin gwiwa da karsashi akan aikinsa. An kuma shigar da case d'in Court kamar yanda Galadima ya buk'ata, abinka da lamarin manya har antsaida washe gari a matsayin ranar da za'a zauna Court d'in. Yinin ranar zubur Galadima baiyi magana da police ko d'ayaba, koda sun buk'aci magana dashi saiya had'asu da Muftahu ko Nuren. Daga k'arshe dai dolensu suna k'yaleshi. ★★★★★★★★ *_⚖RANAR SHIGA COURT_*⚖ Yau ta kasance ranar zaman court, shari'ar su Galadima Ce kuma farko da za'a fara saurara a court d'in, lallai wannan shari'a ta manyace, Dan court d'in ta cika da manyan k'asa wad'anda sunfi kud'i wahalar gani, amma yau gasu available, y'an jaridar ma manya-manya aka bari, k'ananun suna awaje sunyi tururuwa domin rajin nemawa d'an uwansu hak'insa wato Alhaji Auwal fharuk dayake a asibiti har yanzu cikin halin ni y'asu. Mukuwa talakawan gari y'an jiran jin yazata kaya mu sai dai gani a tv☹. Yo Wayaba asibi laya ubanta ba malam ba😬, ai ko babama da babansa aradu🤕. *_Court_* d'in tayi tsit babu abinda kakeji sai gudun fankoki da tarin manya jefi-jefi, dan babu alamun fara'a a fuskar kowa. Daga masarauta dai k'anin mai martaba ne yazo wato Garkuwa Hayatudden Abubakar, sai wasu daga tawagar y'an majalissar Sarki, harda waziri dayazo bisa tirsasawar mai martaba. Daga masarautar su Papi kuwa yarima mai jiran gado mahaifin su Nuren wato Wambai Abubakar Abdul-fatah Wanda yagaji sunan kakansu Galadima marigayi Abubakar kenan. Saikuma wasu daga jiga-jigan masarautar suma. Fitowar alk'alin alk'alai Othman Ibraheem gwannu tasaka dukkan jama'ar Court d'in mik'ewa domin girmamawa a garesa, (dan shima Alk'ali baba uban su babane shima🤭😝). Saida ya zauna sannan yabada izinin kowa ya zauna, Court d'in tayi tsit kowa ya Zubama alk'ali dake karanta takardar k'arar hankali kwance ido, kusan mintuna 3 ya d'ago yanabin Court d'in da jama'ar cikinta da kallo ta cikin eyeglasses nashi daya jawo k'asan ido, d'auke idonsa ya ya maida ga Lauyoyi dake zaune suna jiran kule, suce cas. Gyaran murya yayi yana maida idonsa ga takardar da fad'in “Ina wad'anda suke k'arar da kuma wad'anda akai k'ara? Idan kuma Lauyoyine to na masu k'ara da wad'anda ake k'ara suna inane?”. A tare Baffi suka mik'e shida abokan aikinsa su uku, cikin girmamawa ga alk'ali ya risinar dakai yana mik'a gaisuwa da fad'in “yamai girma mai shari'a sunana Barrister Usman Audu Tsanyawa, nine lauya mai kare Wanda yake k'ara, tare dani akwai Yohan Emanuel, da Bilkisa Ibraheem Musa (kutu melesi su bilyn Abdul anzama lauyoyin novel🤸🏻‍♀😎🤣😜). Bilkisu da yohan suka risina alamar girmamawa. Alk'ali ya jinjina kai alamar gamsuwa, su Baffi suka zaune, lauyan wad'anda ake k'ara shima ya mik'e, ya rissina tamkar yanda Baffi yayi, sannan yace, “ya mai girma mai shari'a sunana Barrister Adam Sadiq Adam, nine lauya mai kare wad'anda ake k'ara, tare dani akwai Barrister Aliyu Sa'adu yaro”. Barrister Aliyu ma ya mik'a gaisuwa ga alk'ali sannan suka zauna. Alk'ali yabama Baffi damar tashi domin yin magana. ALLAH Sarki dattijon kwarai kenan, masu wahalar samu cikin k'asa a halin yanzu, ya gyara hularsu ta lauyeyi dake Kansa, tare da farin eyeglasses d'insa dan rayuwa taja, ijiya duk sun raunana, ya kalli jama'ar cikin Court d'in sannan ya dawo da kallonsa ga alk'ali, yace, “yamai girma mai shari'a! Kamar yanda kowa yasani Muhammad Sameer Saifuddin Abubakar (Galadima) shine yake Neman son sanin miya saka wad'annan mutanen 11 yin gamayya wajen kama surukinsa harsu wahal dashi? Bayan kuma shikeda alak'a dasu bawai surukinsa ba?”. Kai Alk'ali ya jinjina, cikin sauke numfashi yace, “Lauyan wanda ake k'ara gareka”. Barrister Adam Sadiq Adam ya mik'e shima yana fitowa fili, yayinda Baffi Yakoma ma zauninsa ya zauna, Brr Adam Sadiq Adam yace, “yamai girma mai shari'a wace irin tambayace ke fitowa daga bakin lauyan mai k'ara? Ai sune yakamata ayima tambayar minene dalilin shi Galadima Na kama yaran wad'annan mutane 11 yayi Garkuwa dasu yau tsawon kwana biyu? harma da kisan wani a cikin su......... A hanzarce Baffi ya d'aga hannu sama yana mik'e da fad'in “yamai shari'a tambaya akaima lauyan mai k'ara, amsa kuma yakamata ya bamu baya sakko tashi tambayarba”. Hannu Alk'ali ya d'agama Brr Adam Sadiq Adam, yace, “Brr Adam ka gyara, amsa muke buk'ata, kanada dama kaima kayi taka tambayar daga baya”. Brr Adam Sadiq Adam ya risinar dakai alamun ban hak'uri sannan ya gyara tsayuwarsa yana fad'in “Yamai girma mai shari'a akwai abinda ke hannun Alhaji Auwal Fharuk Wanda mallakin su wad'annan mutane 11 ne, shine sukeda buk'atar kar6a”. Baffi yamik'e yana fad'in “yamai girma mai shari'a ko zamu iya sanin minene wannan Abu da suke tuhumar Alhaji Auwal Fharuk akansa, dahar suka kasa mik'ashi ga sharia domin kar6a har sai sunbi ta hanyar nuna k'arfin ikonsu?”. Brr Adam Sadiq Adam yay shiru yakasa cewa uffan, dan ganin tun a tashin farko yana shirin zurmawa. Ganin yak'i cewa komai Baffi ya kuma cewa “ya mai girma mai shari'a idan baza'a samu amsaba ina buk'atar d'aya daga cikin y'an wad'annan tawaga domin ya amsamin tambayata idan shi Barrister bai saniba”. Alk'ali ya jinjina kai yana bada Umarnin tasowar d'aya daga cikin su Alhaji Mansur. Dukfa abinnan dake faruwa Galadima yana kallon komai kai tsaye ta Computer, danshi baizo Court d'inba, babu damar hakan, yana fitowa a gidan police kamashi zasuyi, wannan yasa tukan zaman Shari'a Alk'ali yabada wannan damar ta had'a video call d'in da Galadima zai iya ganin komai da za'ayi kamar yanda IG ya buk'ata bisa umarnin shi Galadima d'in, kamar yanda ya shard'anta ko amasa hakan koya jeho gawar yaro d'aya ko yarinya. Hakan yasa sukai masa babu gardama. Alhaji Abdul-Naseer dake farkone ya taso, ya shiga inda aka tanada domin buk'atar hakan, ya fad'i sunansa da matsayinsa, sannan Alk'ali yabama Baffi damar masa tambayar. Baffi ya k'arasa jikin katakon d'aya shiga tsakaninsa da Alhaji Abdul-Naseer, idonsa a kansa yace, “Alhaji Abdul-Naseer, nasan kana d'aya daga cikin y'an wad'annan tawaga, shin kozaka iya amsa mana tambayar da lauyanku ya kasa?”. Murmushin Alhaji Abdul-Naseer yayi, cikin kwarin gwiwa yace, “Brr Usman, a ganina wannan sirrinmu ne, koma mi muke buk'ata a hannun Alhaji Auwal Fharuk mukeda alak'a dashi ai ba kowaba ko?”. Baffi yashiga jinjina kai yana murmushi, yayi taku d'aya biyu saikuma ya juyo ga Alhaji Abdul-Naseer, yace, “lallai wannan gaskiyane Alhaji Abdul saidai kuma dalilin sanin Court yanada alak'a da samo Alhaji Auwal Fharuk a hannunku, wanda ta silar kama y'ay'anku da surukinsa yayine kowa yasan hakan, saikuma gashi shi wannan bawan ALLAH Alhaji Auwal Fharuk a jiya daya farfad'o dukda baya cikin hayyacinsa, amma yana ambatar sunan Alhaji Halluru da jaddada lallai koda zaku kasheshi bazai bada wannan camera ba, domin shekarunma da kuka d'auka kuna ma rayuwarsa barazana bai bakuba balle kuma yanzu da lokacin Isar da ita ga Wanda akace ya Isar yayi, kenan Alhaji Auwal Fharuk k'arya yayi?”. Da sauri Brr Adam Sadiq Adam ya mik'e yana fad'in “ya mai shari'a wannan ai tamkar titsiyene Brr kema Wanda ake zargi, dan babu yanda za'ai la'akari da mutumin da baya cikin hankalinsa kamar yanda ya fad'a.....”. Shima Baffi azamar dakatar dashi yayi, yace, “yamai girma mai shari'a Barrister Adam bashida hurumin yanke hukunci akan yanayin Alhaji Auwal, sai ya bari bayanin likitoci ya tabatar mana hakan”. Alk'ali yay gyaran Murya da buk'atar ganin likitan dake kula da Alhaji Auwal Fharuk (Abba). Cikin mintuna 3 saiga doctor ya shigo. An sakashi d'ayan wajen, ya fad'i sunansa da aikinsa, sannan Alk'ali yace, “kaine likitan da ke duba lafiyar Alhaji Auwal Fharuk? ”. “eh nine yamai shari'a”. Alk'ali yace, “kozamu iya sanin wani Abu dangane da jikin Alhaji Auwal Fharuk? ”. “kwarai kuwa ya mai shari'a, an kawo mana Alhaji Auwal Fharuk cikin hali irinna suma, amma babu wani alamar duka ko harbi a jikinsa, saidai bincikenmu ya nuna an shak'a masa wani Abu. Daya saka numfashinsa Nisan zango, sai ajiyane bisa hukuncin ubangiji ya farfad'o, wad'annan kalamai sune abinda ya farka dasu a bakinsa, kuma kwakwalwarsa ras take, abinda aka shak'a masanne kawai bai sakesaba har yanzun, danma yanada jini mai k'arfine”. Cikin wad'anda suke zaune ma'aikatan Court d'in d'aya yaje ya kar6i wayar doctor da yay recording ya kaima alk'ali. Alk'ali ya kunna recording ya saurara, ya ajiye wayar gefe da sallamar doctor cikeda gamsuwar abinda yaji. Sannan shima yabada Umarnin sanin ita camera ta micece?. Baffi yakuma mik'ewa tsaye yana gyara k'atuwar rigarsa, yace, “ya mai shari'a, ita wannan Camera da wad'annan gamayyar mutane suke farautar rayuwar Alhaji Auwal Fharuk a kanta tanada alak'a da Muhammad Sameer Saifuddin Galadima ne, itace kuma musabbabin d'aukar yaran wad'annan mutane 11 dayayi yake tsare dasu a gida mai labba 67 dake anguwar tudun na ALLAH a tsakiyar binni, damin camera dai k'unshe take da abinda ya faru da tsohon Sarki dake jiyya a India, wato Mai martaba Saifuddin Abubakar tsawon shekaru 26 kenan ba'asan wad'anda suka aikata masa abinda ya kaisa da jiyyarba”. Turk'ashi, kallon kallo kenan, to lallai shine aka shigayi a wannan Court, nanfa k'ananun magana suka fara tashi tsakanin manya, Court ta harmutse da hayaniya babu maijin zancen wani, saida alk'ali ya tsawatar sannan akayi tsit. Inda kuma a gefe tsantsar rud'ani da rikita ta mamaye su Alhaji Balala, ko kad'an basuyi zaton shigowar wannan maganar da wuri ba cikin shari'ar, shima kansa lauyansu haka, tunda wawantar dasu Galadima yayi akan Shari'ar ta shafi d'aukar Alhaji Auwal Fharuk ne da farko. Alk'ali da shima kansa ya shiga wani yanayi ya buk'aci ganin Muhammad Sameer a Court. Baffi ya kuma mik'ewa yana fad'in “ya mai shari'a, ai Muhammad Sameer Saifuddin Galadima bashida ikon zuwa court a yanzu, domin kuwa yana can tsare da yaran wad'annan mutane 11 ne, kuma yana fitowa y'an sanda zasuyi ram da shine a matsayin mai laifi babbama kuwa, dan yanzu akwai laifin garkuwa da yara d'in a kansa, saidai munada hanya sassauk'a ta had'a wannan adalar kotu da Galadima kai tsaye”. Alk'ali ya bada damar hakan. Dandanan kuwa aka had'a Galadima da kotu, Wanda dama shi tuni yana ganin duk abinda sukeyi, sunedai basa ganinsa. Galadima dake zaune a falon gidan da yake tsare dasu harun ya mik'e tsaye domin girmamawa ga alk'ali, sannan ya gabatar da sunansa kamar haka, “ya mai shari'a sunana Muhammad Sameer Saifuddin Abubakar, ma'aikaci a hukumar bincike ta DSS”. Wani sabon kallon kallon aka koma, Wanda yaja hankalin mutane fiyema dana d'azun, hattada y'an masarautar gagara badau basusan da wannan aiki Na Galadima ba. Alk'ali ya kuma tsawatarwa, sannan ya maida hankalinsa ga Galadima yana fad'in “To Muhammad Sameer minene alak'arka da iyayen yaran dakake rik'e dasu, danmu ka rikita mana tunani, da farko kallon Criminal muke maka, saikuma gashi sunanka yafito a d'aya daga cikin manyan hukumominmu Na tsaro masu muhimmanci?”. Murmushi Galadima yayi yana gyara tsayuwa, ya hard'e hannayensa a k'irji yana sauke numfashi da cije lips, yace, “ya mai shari'a wannan labarine mai tsawo, amma tabbas abinda lauyana ya fad'a shine gaskiyar zance, Camera dake hannun Alhaji Auwal Fharuk itace babbar alak'ar dake tsakanina dasu, wadda nad'au tsawon shekaru akan nemanta, sai a shekararnan ne cikin watanni shida nasamu labarin inda take dukda banida tabbacin ita d'ince, bansan mike cikin camera d'inba, amma su Alhaji Balala duk sun Sani, tunda har suka iya salwantar da rayuka da yawa akanta, shi kansa Wanda suka hara a yanzu ALLAH ne kawai yasaka yanada tsawon rai, amma da tuni sun kasheshin, ni kaina rayuwata tasha hare-hare iri-iri harda jariran yarana da aka sace kwanaki 7 kacal da zuwansu duniya”. Alk'ali da yay shiru yana sauraren Galadima yaja dogon numfashi yana ta faman jinjina kai tamkar k'adangare yaga abinci mai manja😱🤭. Yace, “lallai wannan Court tana buk'atar jin cikakken bayani daga Muhammad Sameer Saifuddin, dan haka ta d'aga wannan k'ara zuwa nan da kwanaki uku masu zuwa, kotu tana bama y'an sanda Umarnin subar Muhammad Sameer Saifuddin ya fito daga wannan gida a ranar da Court zatayi zama Na gaba batare da koda masa hararaba, sannan kuma kotu ta bada Umarnin a cigaba da tsare su wad'annan mutane guda 11, likitoci kuma su cigaba da bama Alhaji Auwal Fharuk kulawa ta musamman dan shima kotu Na buk'atar ganinsa a zama Na gaba saboda son sanin mike cikin camera d'in”. Alk'ali ya buga gudumarsa yana mik'ewa. Gaba d'aya kowa ya mik'e har alk'ali ya shige. Galadima yay wani k'asaitaccen murmushi yana zaunawa cikin kujera bayan shigewar alk'ali. Muftahu, Nuren, dasu Harun dake zaune gefe suma suna kallon komai tun farkon Shari'ar duk sunyi mutuwar zaune tun lokacin da Galadima yafad'i kasancewarsa cikin hukumar C.I.D. Ameer ne kawai yay murmushi yana k'amewa da salute d'in Galadima. Shima baki sake su Nuren suka bishi da kallo suna nunashi alamar dama yasani shi?. Murmushi yay musu har hak'oransa Na bayyana ya had'e hannayensa waje d'aya alamar tuba a garesu. ★.....................................★ Yau kam Galadima wani farin ciki Na musamman ya tsinci kansa a ciki, ya shige d'akin da yake matsayin nasa a yanzu ya fad'a gadon yana rungume filo idonsa Na zirar da hawaye, ko a haka aka tsaya lallai yaci nasara, dan ya nunama su Alhaji Abdul-Naseer d'an zaki ya girma. Wayarsa dake saman gadon a can gefe yasa hannu ya janyo, ya kunnata, massages ne sukaita shigowa a jere-jere kamar jira, bai bud'e ko wanneba ya shiga binciko number Munaya, ya dad'e yana kallon Number amma ya kasa dialing, yaja wasu seconds kafin yatsansa ya sauka akan number ya danna kawai. Munaya Na zaune a falo tare da su Ayusher da kullum sai sunzo, d'an kunne ne ya shige cikin jikin Amaturrahman yanata cin jikinta basu saniba, sai yau da an ta6a fuskarta koyaya saita fashe da kuka, Munaya tarasa mike damun yarinya, dukta rikice ita kanta, saida laraba tace ta bata nono, tana kwantar da ita ta wajen kunnen sai takuma d'ad'ewa da kukan da Munaya ke jinsa har cikin jini, d'agota tayi tana duba wajen, Laraba tace, “Anya ba kunenta ke ciwoba?”. Munubiya dake kusada Munaya ta amshi Amaturrahman ta kifata a cinyarta tana dubawa, sai taga d'an kunne ne ya shige Ashe duk bayan kunnen yayi ruwa, tsoro ya kama Munubiya, cikin zaro ido waje tace, “innalillahi, d'an kunne natacin kunen yarinya bamu saniba”. Da an fara k'ok'arin ciremata saita kuma fashewa da kuka tana mimmik'ewa, gwaggo safiya data shigo yanzu saboda jiya ta iso akan abinda ya faru da Abba, ta k'araso cikin falon tana fad'in “mike faruwane?”. Bayani feena tai mata, gwaggo safiyya ta kar6i Amaturrahman tana cewar asamo mata ruwan d'umi da k'aramin handkerchief. Ana cikin hakane Galadima yayi kiran Munaya, tashitai tabar wajen tana had'iye kukan dake shirin taho mata saboda tausayin yarinyar. 'Dakinsu ta shiga, ta fad'a saman gadonsu ta kwanta tana amsa wayar. A hankali Galadima ya sauke ajiyar zuciya yana gyara kwanciya. Murya can k'asan mak'oshi yace, “babu fad'a miya kawo gaba yalla6iya?”. Murmushi Munaya tayi tana share hawayenta. Tace, “Kodai Kaine za'aima wannan tambayar?”. Jimm yayi saboda jin muryarta ba ayanda yasaniba. yace, “mike faruwa kike kuka?”. Mamaki ya kama Munaya, ta Yayama ya gane kukan take, cikin k'ok'arin kare kai tace, “ba kuka nakeba yalla6ai, ina yini”. bai amsa gaisuwarta ba yace, “kina wasa da sanin danai miki ko?”. Yay maganar cikin d'an kausasa murya. Munaya sai bataji dad'iba, tace “kayi hak'uri, dama Amaturrahman ce d'an kunne ya shigema a jiki taketa kuka, amma gashi can suna cire mata d'an kunnen”. Babu shiri Galadima ya tashi zaune yana fad'in “k ya akayi har d'an kunne ya ringa cin jikinta baki saniba? Anya kuwa kinason yarannan Munaya?”. Wani haushine ya kamata, tama rasa mizata Ce masa. Shima bai jira amsartaba yace, “maza ki tashi kuje asibiti a dubamin yarinya, karkuce zakuyi gangancin cire mata a gida wata matsalar ta biyo baya”. “Uhumm”. Kawai Munaya tace ta yanke wayar. Ta jefar da wayar gefe tana hawaye, shi kawai yaransane damuwarsa, harma zaice yafita sonsune dazai dinga jifanta da bata sonsu kulum-kullum, itafa wannan Abu yafara kaita bango wlhy. A can kuwa shima Galadima duk sai yaji ya damu, jiyake tamkar yay tsuntsuwa yafita yakai yarinyarsa asibiti da kansa, amma babu damar hakan. Ya dad'e jikin window tsaye yana kallon mutane daketa zirga-zirga a anguwa da police d'in dake zagaye da gidan har yanzu. Fita munaya tayi dan ganin ko ancire?, ta iske an cire ana gasa kunnen, Amaturrahman taci kuka harta koma ajiyar zuciya, Gwaggo Safiyya tace, “zoki zauna kibata tasha sai'a k'arasa gasawar”. Zuwa Munaya tayi ta zauna tana kar6ar Amaturrahman. K'in k'ar6ar nono tayi, sai ajiyar zuciya taketayi, Laraba tace, “yaranan zuciya irinta Magajin gari suke da ita, yanzu inba sa'a ba bazatashaba”. Dariya su Ayusher sukayi. Dak'yar dai Munaya ta turama Amaturrahman nono abaki ta kar6a. Akad'an kuma gasa kunnen dayay uwar huda naman wajen yafita sosai, k'ofar tazama babba. Munaya dake kallonta tasaka hannu tana goge mata zufar data taru mata a goshi, saikace wata babba. Galadima yanata kiran Munaya yaji kosun tafi asibitin amma bata d'agaba, dayake ta bar wayar a d'akinsu. Saida Ayusher taje d'akin ta gano, ta d'akko da sauri ta kawo mata tana saka mata a kunne. Maganarsa kawai munaya taji yana fad'an ina ta ajiye wayar. Ajiyar zuciya ta sauke tabashi hak'uri kawai, dan bata buk'atar jan maganar. Yace, “kunje asibitin?”. Munaya tace, “An cire mata ai, babu wata matsala tunda bai ta6a cikiba”. Ca yay ta d'auka hoton wajen ta turo masa yagani, kamar tace bazatayiba sai kawai ta cire wayar ta katse kiran, hoton wajen ta d'auka ta tura masa”. Tausayin yarinya ya kamashi ganin yanda wajen yay cinye sosai, Yakuma kiran Munaya yana jaddada mata karta sake akuma sakamata wani d'an kunne. To kawai ta amsa masa dashi dan a zauna lafiya. ..............................★ Tun daga ranar Munaya bata sake jin Galadima ba, saboda yayi busy da yawa akan shirye-shiryen shari'ar dake gabansu, dan fatanshi wannan zaman yazama zama Na k'arshe insha ALLAH. Alhmdllh jikin Abba anata samun haske sosai, dan sauk'i yana samuwa iya gwargwadon iko. *_RANAR DA ZA'A KOMA KOTU_*................✍🏻 Hummm😬 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻_* [8/3, 3:39 PM] +234 813 221 4515: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣8⃣ .................Yauma dai kotun ba'a cewa komai, wad'anda ma basuzo zaman farkoba yau sunzo, Dan su sir Isa duk suna wajen da muk'arabansa, hakama tawagarsu Tanderu, Dan suma lauyansu a cewarsa yau yazo da sabon shiri, ranarma an mamesa ne kawai. Galadima yagama shirinsa tsaf cikin wani lallausan yadi sky blue dayasha d'inkin boda, Dan rigar iyakarta Rabin cinyarsa, kayan sunmasa k'yau matuk'a, danya fito ainahinsa Na jinin Hausa Fulani, ya Mirza hularsa sky blue itama, fuskarnan tayi fayau Dan hardasu gyaran fuska yayi abinsa, danma ya tabbatarma mak'iya yana cikin farinciki fiye da zatonsu, yana cikin saka sock's Nuren ya lek'o yana fad'in “Brother ka hanzartafa mun makara”. “umhum” kawai yace masa yacigaba da saka kayansa a tsanake kamar yanda yafara, danshi komai saurin dazaiyi akan Abu to anutse zaiyi abinnan, ganin haka sai kawai Nuren ya ida shigowa, ya durk'usa gabansa yana kama k'afar daya sakama sock's d'in ya saka masa takalmi. Baki Galadima ya tsa6e yana cewa, “kaifa shegen gaggawane dakai wlhy, ni bansan INA kuka kwaso halinnanba, haka Momma da Aunty Mimi suke, komai kunfison mutum yanayi kamar wani mazari”. Nuren ya sanya dariya yana saka masa d'aya takalmin, yace, “to sokake muke Abu kamar marasa laka a jiki? Munaya dai kam tana fama...” Hararsa yayi, hakanne ya hana Nuren k'arasawa, Galadima daya wani tsaresa da ido yace, “Tana fama da k'aniyarka”. Nuren ya mik'e yana fad'in “oho maka dai, mu ka fito su sarkin mota tuni sukazo”. Mik'ewa yay ya d'auki turarensa Na kullum a bag d'in daya had'o kaya ya fesa, k'amshin ya gauraye ko ina, waya d'aya ya zura a aljihu ya fito. Su Ahakam duk shagala sukayi da kallonsa, a ransu suna matuk'ar yaba tsarinsa, komai nasa abin birgewane, kamar yanda ya saba haka yabasu hannu da kansa sukayi musabaha dukda suna nok'ewa alamar jin kunya da girmamawa a gareshi, shikam babu ruwansa, inhar bakasan halinsa bane dolene tashin farko ka jefeshi da kalmar girman kai. Su Farhat ma suka gaisheshi cikin risinawa, wani miskilin murmushi yamusu yana d'aga musu hannu kawai, ya kalli Saleem tare da masa nuni yabama kowa kayansa. Saleem ya amsa da cewar “ok boss”. Bag d'in da wayoyinsu ke ciki ya d'akko, amma sai sukace sukam ya barsu, Dan inhar ba'a yanke hukunci ba zasu dawo su cigaba da zama dasu, Dan zama da Galadima akwai dad'i, kuma ko an yanke hukuncima masarauta zasu bishi. Shi dariyama abin ya bashi, hakanne yasakashi bubbuga kafad'ar Yassar dake kusa dashi yana sakin murmushin da har hakwaransa ke bayyana, ya wucesu yana sauka daga benen cikin takunsa Na birgewa. Suma duk binsa sukayi a baya, komai nasa Saleem ya tattaroshi, dan bazai sake dawowa gidanba koda ba'a yanke hukunci ba kuwa. Harun dai anyi laushi matuk'a, dan maganarma yanzu ba iyayin mai k'arfi yakeba, saboda saiya gadama yakecin abinci, babu kuma mai sakashi dole yaci. Cikar k'ofar gidan tabama Galadima mamaki matuk'a, yakuma d'aure fuska tamkar bai ta6a dariya ba, musamman yanda duk aka zubo masa ido, a Bayama an kallesa balle yanzu da yayi abun kallon, y'an sanda da dogaransa da suka zo d'aukarsa tun d'azun sai k'ok'arin hana y'an jarida dakeson zuwa ga Galadima sukeyi, amma suna k'ok'arin kutsowa. Tsaye Galadima yayi ya zuba dukkan hannayensa a aljihu, saida yaga shigarsu Rahma mota dasu alhaji darma sannan yanufi inda sarkin mota ya bud'e masa, y'an jaridar daketa masa tambaya ko kallo basu isheshiba ya shige mota abinsa, yayinda Muftahu ya zauna gefensa, Nuren Na a gaba. Mortar y'an sanda Na a gabansu da Bayansu, a haka akayi tafiyar. Sauran y'an sandan da aka bari suka shiga gidan domin d'akko gawar Ahmad, amma sun bincika lungu da sak'o babuma alamar an cutar da wani, sai harbi guda d'aya daya shiga jikin bango, (shima Wanda Galadima yayine sanda ya tsoratasu da cewar ya kashe Ahmad), basu samu komaiba dazai nuna Galadima d'an ta'addane, sai suka fito suna kulle gidan, amma basu tafiba harsai kotu tabada damar hakan. ............................★ Sun Isa Court d'in, inda Galadima da Nuren da Muftahu ne kawai suka Shiga, yaran dasu Alhaji Darma an kaisu wani d'akine kusada wajen. Takun takalman Galadima dake tafiya cikin tsantsar izza da nuna jinin mulki ya saka dukkan jama'ar kotun zuba masa idanu, shikam ya had'e fuska tamkar hadarin gabas Na tsakkiyar ogusta dabaya d'aga k'afar zubar ruwa, kallon kowa bayayi, gashi ya toshe idanu da Google eyeglasses d'insa da babu mai kallon kwayar idonsa. A kujerar farko irin wadda su Alhaji Mamman ke zaune shima aka nuna masa shida Nuren da Muftahu. Wani zama yayi dake tabbatarma da mak'iya shid'infa sarakine, gaba da baya kuma. Hakan ya k'ona zuciyar su Alhaji balala matuk'a, amma babu yanda zasuyi. Zaman Galadima babu jimawa saiga alk'ali ya fito, kowa ya mik'e domin girmamawa, saida ya zauna sannan duk aka zauna. Kotun tayi shiru kowa ya zubama alk'ali idanu, yagama dube-duben ta kardun gabansa sannan ya d'ago ido yana kallon jama'a, yace, “Yau shari'ar zata tafine kai tsaye batare da shigar lauyoyi Na kowanne 6angare a tsakiyaba, Dan haka muna buk'atar Wanda yay k'ara, da wad'anda ake k'ara a gaban kotu”. A hargitse su alhaji Sageer suke kallon kallo, hakama lauyansu dukya shiga rud'ani, saboda mugun shirin dayayo yau akumace ba haka za'ayiba. Shikam Galadima wani mugun murmushi yayi yana kallonsu Alhaji mansur d'in damusu wata inkiya da yatsu biyu alamar a kafta, sannan ya mik'e. Dole suma duk suka mik'e inda aka buk'aci ganinsu, dukda wajen yamusu kad'anma. Alk'ali ya kalli galadima. Yace, “kaine Wanda kai k'ara, Dan haka munason jin shin minene mafarin wannan takun sak'a kai tsaye?”. Murmushi galadima yayi, ya cire eyeglasses d'in idonsa ya saka cikin aljihu, tareda zaro handkerchief ya goge fuskarsa, yasa hannayensa biyu ya dafe katakon gabansa yana jifan waziri mahaifin Harun dawani mugun kallon daya hargitsa y'an cikinsa da tunaninsa, hakanne yasaka mutane kallon waziri suma, duk sai yaji ya muzanta. Galadima ya ta6e baki yana janye idonsa dad'an cije lips, cikin k'asaitacciyar muryarsa yace, “ya mai shari'a labarina mai tsawone kwarai da gaske, sannan cike yake da abubuwan ban mamaki da takaici masu tarin hargitsi, duk da nasan kowa yasan sunana amma zan sake maimaitawa, sunana Muhammad Sameer Saifuddin Abubakar, gidan sarauta Na fito, mahaifina shine tsohon Sarki da k'addarar ciwo ta kwantar tsawon wasu shekaru, amma lallai da sanadi, wannan kuma sanadin shine Na d'auki tsawon shekaru tundaga tasowata har zuwa yau ina nema. tun daga lokacin dana mallaki hankalin kaina nasan minene matsalar mahaifina natashi da burin d'aukar fansa, sai dai kuma tayaya? Wannan shine yayta wahalar da Muhammad Sameer a tsawon shekaru”. Galadima ya k'are maganar idonsa Na ciko da hawaye, yay murmushin takaici yana jinjina kansa da had'iye hawayen. Hakanne yasaka jikin wasu fara yin sanyi, musamman wad'anda suka k'ullaceshi da farko. Galadima ya cigaba da fad'in, “Ban taso maraya ba, amma nayi rayuwa irinta marayun, ALLAH shine gatana saikuma mahaifiyata da kakana da suka tsaya tsayin daka wajen tsayamin nazama jarumi wajen sanin wahalhalun rayuwa Na yau da kullum, duk Sana'a mai wahala kad'ance banyitaba a k'asar daba tawaba, gakuma gefe ana gwagwarmayar Neman ilimi, ga burin son sanin suwaye suka durk'usarmin da mahaifi?, ban cutar da kaina wajen nutsuwa Na fahimci rayuwa ba, hakama nabama karatuna muhimmanci saboda k'aunarsa da nakeyi, duk da banida burin yin aiki a k'ark'ashin kowa, Alhamdllh yanzu haka inada Company Na had'aka da duk shekarar duniya yake fidda wayoyin Hannu da computers dakan zagaya cikin duniya, ina alfahar da samun cikar burina sosai, Na dad'e ina bulayin Neman hanyar bincike akan abinda yafaru da Abie na, alokacin mutum d'ayane zuwa biyu ke bani gudun mawa, wato lauyan mahaifina, baffina Barrister Usman Audu, sai kakana Sarki Abdul-fatah. Ganin inata wahala sanan babu wani haske a cikin lamarin sai suka bani shawarar mizai hana a nemamin aiki k'ark'ashin wata hukumar tsaro, da farko ban aminceba, Dan irin wad'annan ayyukan basa wani birgeni, hasalima haushin masu yinsa nakeyi, Dan sun gaza binciko Wanda ya cutarmin da Abie na. A tashin farko dana nuna banaso Papi da Baffi sun k'yaleni, basu sake min magana ba, sai wata rana kwatsam wani Abu yafaru anan Nigeria, wasu y'an ta'adda sukayi mummunar 6arna a sirrin gwamnati, k'ark'ashin hukumar DSS. wannan 6arna ta rikita Nigeria sosai a lokacin, shekaru 10 kenan inhar ban mantaba, a lokacin nagama bautar k'asata anan Nigeria ina shirin komawa india, bansan ya akayi sukasan nasan Computer ba, har masarauta akazo aka rok'i mai martaba akan Na taimakesu. Da farko kam naso bijirewa amma babu abinda iyayena zasuce nayishi banyiba inhar bai sa6a shari'a ba, nasanma bazasu sakani wannanba, bisa umarnin mai martaba Na amince da gwadawa idan zan iya, haka akaje dani headquarters d'insu, tun hawan Computers d'in danai a tashin farko Na gane da had'in kan waaunsu aka kwashi bayanan, sannan masu kula da Computers d'in sunada buk'atar k'arin ilimi ma gaba d'aya. Cikin sauk'i Na d'akko bayanan da aka d'auka Na dawo musu dashi, sannan nasaka musu securitys masu tsaurin gaske daba wani mahaluki dazai kuma musu irin wannan kutsen. Ni ban d'auki abinda nayi matsayin komaiba, amma agaresu sun girmamashi, sunkuma biyoni har gida da rok'on kasancewa a cikinsu amma nak'i Sam, nama tattara Na koma India, Ashe sunata bibiyata ta wajen kakana, to shima dama yana burin nayi aikin, Dan haka yabasu goyon baya, sannan yaje har India ya sameni da batun, ya nunamin ta wannan hanyarne kawai zan iya binciko abinda ya faru da mahaifina cikin sauk'i, hakama Baffi ya fad'amin a lokacin, Na zauna nayi nazari dakuma samun kwarin gwiwa daga Mahaifiyata. Rana d'aya sai nima naji yakamata Na amince, Dan haka Na amince, tundaga lokacin nashiga cikin hukumar CID nima, saidai ina musu aikine cikin sirri, a hukumarma ba kowa yasan daniba, tunda ni komai ta computer nake gudanar dashi. Sir Isa Maharazu shine ya taimaka min wajen binciko file Na binciken case d'in mahaifina, Wanda tun kusan shekaru 8 mai kula da case d'in ya rasu, Wanda kuma suke ta fannin y'an sanda suma sukayi shiru, daganan aka ajiye case d'in gefe kawai. Tun a file d'in nafara cin karo da sunayen wasu daga cikinsu Alhaji Lawan tanderu. Nasha mamaki kwarai da gaske amma sai banyi wani yunk'uriba, ina wata shida da aiki wani yaso min kutse a cikin Computer, ta silarsa nagano uban gidansa, har zuwa Kansu Marigayi Alhaji Labaran kachia. Tundagafa wannan lokacin saina tsananta bincike da kwakwalwa dakuma tannin aiki, bisa taimakon sir Isa, mun baza yara cikinsu Tanderu batare da sunsaniba, kullum kuma cikin bin diddigin motsinsu suke. Kwatsam sai Tanderu ya rasu sanadin had'in mota, babu jimawa shima Alhaji Labaran khacia ALLAH yamasa rasuwa sanadin rashin lafiya. daga nan saina d'an dakatama gaba d'aya da wani bincike Na koma gefa Na zuba musu ido kawai. Saida Na d'auki kusan shekaru biyu ban sake wani yunk'uriba sai kwatsam muka wayi gari mijin Yayata Haneefa yayi had'arin Mota, saidai kuma a ranar ne aka turomin massage daya nuna accident d'in nashi akwai saka hannu a ciki, dayake bai rasuba a lokacin sai a asibiti bayan awanni uku da kaisa, Alhaji shehu Darma abokinsa ne Na kut da k'ut sannan d'an uwansa, Dan haka yana tare damu a wajen, saina matsanta akan tambayarsa kozai fad'amin akan miya faru dashi kafin had'arin? Bai iya cemin komaiba sai murmushin k'arfin hali da yayi yana kallon Alhaji shehu har numfashinsa ya k'are, wannan kallo ya tsayamin a rai sosai, Dan nagaza mantawa dashi, abinda Yakuma k'arfafa min zargin Alhaji shehu shine Aunty Mimi Na fita daga takaba sai Yace yanason aurenta, nine Na hana, nama tattarata gaba d'aya itada y'ay'anta Na maidasu india, dukda dangin mahaifin yaran sunso d'aukarsu suma. Dama can lokaci-lokaci Alhaji shehu yakanbi mijin Aunty Mimi suje duba Abie, dan haka ko bayan rasuwarsa bai daina zuwaba, abinda na fara fahimta shine Samha d'iyar marigayi tana tsoron Alhaji shehu, amma shi yana tsananin nuna mata kulawa dayin kaffa-kaffa da ita a gaban mutane. Wannan ma yasa na kuma saka ido a kansa, abinda Na fara karo dashi shine Alhaji shehu yana tursasa Samha ta hanyar mata barazana akan ta d'akko masa wasu sirrikana”. Galadima ya murmusa cikin takaici yana gyara tsayuwa da goge fuskarsa da handkerchief. Yaciga da fad'in, “Tunda Na fahimci hakan saina jata a jikina, nakuma dinga ajiye mata dukkan abinda yasaka ta d'akko, itako data gani saita tura masa saboda tsoron barazanar da yake mata. Suma sauran Na cigaba da bibiyarsu suda ayyukansu, so banida matsala da sauran mugayen halayyarsu, nidai kawai wadda ta had'amu nakeson Sani, Dan Na gano sun gana da mahaifina ana gobe abinda ya sameshi zai sameshi, kuma yafito daga d'akin tattaunawar ransa a 6ace. Batanci da akaimin a shekara d'aya data wuce cikin jaridar manuniya shine mafarin yalwatur haske a matsalolina, dukda Na fahimci ankai tsawon shekaru ana bibiyar dukkan al'amurana, kuma inhar Nazo k'asarnan kullum cikin bibiyata ake, domin rufe bakin mak'iyana Na auri wadda sukaso sakawa a matsalar dabatajiba bata ganiba, wadda a yanzu Alhmdllh itace uwar y'ay'ana, nasan hakan ya girgizasu a lokacin kwarai da gaske, adalilin zama da ita nama fahimci abinda ban fahimtaba da farko, Dan da Duk zargina ko da itane aka had'a kai wajen Neman 6atamin suna, amma sainaga dukba haka baneba, ya mai shari'a Alhaji Auwal Fharuk sai shine surikina mahaifin matata, kuma anyi yink'urin kasheshi watanni kusan 7 da suka shige, saidai ALLAH ya k'addara yanada sauran kwanaki a gaba, bisa dalilin yun k'urin kisansa ne kuma Na fara karo da alak'ar case d'in mahaifina dashi, hakan kuma tafaru bisa sanadin matata, data dinga zak'ulomin wasu masu alak'a da mahaifinta kuma Na jikinsu tanderu, irinsu Mamman k'afur, Alhaji Halluru, saikuma daga baya ga SD, wato Alhaji shehu Darma, Wanda shine aka saka yake bibiyar Alhaji Auwal Fharuk yana masa barazana, satar yarana da akayi a ranar sunansu ta kawo bayyanar aminina d'an uwana cikin case d'in mahaifina daban ta6a tunanin kasantuwarsa a cikiba, wato Harun d'an gidan waziri, shine wazirin mahaifina shine kuma wazirin Sarki Na yanzu, ina cikin rud'anin Hakan saikuma ga Alhaji Rabilu ya bayyana a gareni shida Badi d'a ga mai dokuna a masarautarmu, Wanda tun ina k'arami Na sanshi, amma daga baya ya 6ata 6at. Bayanan wad'annan bayin ALLAH da bincikena Na had'a suka tabbatar min da zargina akan wad'annan mutanen, nasan abune mai wahalar gaske samunsu cikin sauk'i da fahimtata da duniya zatayi akan zargin danake musu, shiyyasa naza6i yin Garkuwa da yaransu bisa tursasasu tilas sufad'i abinda ke ransu da Wanda suka aikata. Dukkan Wanda ya shigo cikin labarin nan nawa akwaishi a wajennan, mijin yayatane kawai bayada rai sai mahaifan Badi, dakuma wasu daga cikinsu da sukabar duniya, Dan haka ina rok'on wannan kotu data nemo dukkan Wanda Na ambata domin jin ta bakinsa”. Alk'ali ai yama kasa magana, sai kad'a kai kawai yake mamaki da al'ajabi Na cinsa, yayinda kotu tayi tsit kowa yana k'ullawa da kwancewa da tausayin Galadima, irinsu Alhaji Halluru kam ai cikine ya d'uri ruwa, sunsan dai tasu tagama k'arewa kam, Dan yau ranar bankad'a Ce da walle-walle. Alk'ali yad'anyi rubuce-rubucensa sannan ya buk'aci ganin Badi da Alhaji Rabilu, Galadima kuma yaje ya zauna. Alhaji Rabilu da Badi sun bayyana a gaban kotu, hakan ya kuma hargitsa hanjin cikin Waziri, yana mamakin dama Badi bai mutuba? Amma su hak'ilu sukazo sukace ya mutu a wancan lokacin, dan agabansu mai besfa ya kad'eshi, innalillahi ya shiga ambata a zuciyarsa, sai zufa ke jik'eshi, sauk'insa ma akwai malun-malun da rawani a jikinsa, Abba Hayatudden kallonsa kawai yake da tsantsar tsana da mamakinsa. Duk yanda Badi da Alhaji Rabilu sukaima Galadima bayani haka suka maimaita a gaban kotu, wasu harda hawayen tausayinsu suke matsewa, Alk'ali yace, a kawo Alhaji Auwal Fharuk Dan Badi yaga idan shine yabama camera. An kawo Abba, Wanda Alhmdllh jikinsa yayi sauk'i sosai, saidai abinda ba'a rasaba Na k'arfi, kallo d'aya Badi yayma Abba ya ganeshi Dan bai canja masaba sai canjin girma irinnan shekaru, hakama Abba ya gane Badi sarai Dan shima d'in bai canja masanba, aiko suka rungume juna kowa yana hawaye, Abba yana fad'in “Bawan ALLAH Dama baka mutuba a waccan ranar?”. Shima Badi cikin kuka yace, “ban mutuba, sai daga baya ne Na farfad'o a wajen”. Alk'ali ya ankarar dasu cewa a kotu suke, kotu kuma Na buk'ar jin bayani daga bakin Abba, ta Yaya Camera ta dawo hannunsa?. Abba ya dai-daita tsayuwarsa sannan ya gabatar da kansa ga kotu, ya d'ora da fad'in “shekaru 22 kenan da suka shud'e wannan camera take a hannuna ranka ya dad'e, nakuma sametane ta hanyar kad'e wannan bawan ALLAH danayi da abin hawana a wancan lokacin, saboda ya shigo hanya yana matsanancin gudun dabansan mafariba sai yanzu danaji a ya fad'a a gaban kotu. bayan na bigeshi numfashinsa Na Nuna alamar bankwana da gangar jikinsa ya d'auki wannan camera yabani acikin akwati da sunan amana, yakuma ambatamin sunan wad'anda zanba kamar yanda yafad'a, daganan numfashinsa ya tsaya cak da aiki, ina cikin k'ok'arin taimakonsa saiga wasu mutane da gudu da makamai sun dosoni, tsoro naji, Dan inada tabbacin shima sune suka biyoshi, saboda son isar da amanar daya bani inaji ina gani badan nasoba Na tsallakesa Na gudu, Dan nasandai zasu iya kwatar abinda yabani d'in. tunda camera d'in nan ta dawo hannuna ban sake barci mai dad'iba, kullum burina da tunanina tayaya zan Isar da amanarta Na huta, tsawon shekaru ban ta6a fuskantar wani k'alubale akanta ba, Dan ko iyalina babu Wanda yasan da zamanta a hannuna, matata tasha tambayata idan taganni cikin damuwa amma banta6a fad'a mataba, kwatsam cikin laluben Wanda zan bamawa sai Marigayi Alhaji Abdul-hakeem Uba tsohon Governor d'inmu ya fad'omin, Dan ganin yana auren d'iyar tsohon Sarki wadda tana d'aya daga cikin wad'anda akace nabamawa, to lallai anan Alhaji shehu SD yasan Camera Na hannuna, Dan tabbas yaji zancen da mukayi da Alhaji Abdul-hakeem d'in ta hanyar la6ewa, aranar da mukayi zan bama Alhaji Abdul-hakeem camera ya damk'ata ga matarsa sai aka samu akasi wani aiki ya tasomin Na manta ban fito da camera ba, amma mun had'u da shi marigayi Alhaji Abdul-hakeem Na bashi hak'uri da sanar masa uzirina, shikuma SD a tunaninsu nabama Alhaji Abdul-Hakeem wannan camera, shine suka hari rayuwarsa da nufin kar6a kafin ya kaima matarsa, inaga daga baya da suka fahimci babu Camera d'in a hannunsa shine suka juyo kaina. Sunta matsama rayuwata da barazana iri-iri, kiran waya da sauransu, duk number da suka kirani da ita gobe bada ita zasu kirani ba, hakkane ya sakani ware sim card guda kawai dansu, babu Wanda ya sanni dashi, sai matata Dana saka number cikin wayarta batare da itama tasan hakanba, nayi hakanne saboda watarana koda ALLAH yabasu nasarar kasheni d'in. A lokacin da akaima yarana 6atanci da Galadima lallai hankalina ya tashi matuk'a, amma daga baya danayi nazari saina gano maybe su SD ne suka aikata hakan domin 6atamin suna, hukuncin ALLAH kuma saigashi mai martaba Sarki jalaludden da mai martaba Sarki Abdul-fatah sunzo nemawa d'ansu Galadima auren yarinyata da abin yafaru akanta, dukda a 6adda kama sukazomin ni sarai Na ganesu, amma ko y'an uwana ban sanarmawaba, abinda yabani k'arfin gwiwar aurar musu da yarinyata shine Isar da amanar hannuna cikin sauk'i, saikuma aminin mahaifina Baba mai kanwa yace nabasu, Dan shine kawai yasan da zaman Camera a hannuna, shima bani Na sanar masaba, bankuma San a ina yajiba. A randa za'akai y'ata gidan mijinta a ranar Na saka wannan camera da takarda cikin wani kwali Na sakashi a kayanta batare da tasaniba, bansaniba kota gani? Dan cikin gifts d'inta data samu a hannun abokan mijinta ranar dinner d'in auranta Na sakashi, nabama d'an uwantane Abdul-Hameed babban d'ana yabata batare da shima ya san minene a ciki ba. Hikimata anan idan tagani tabama mijinta batare da kace Na ceba. SD bashikad'ai ke bibiyar rayuwata ba, Dan akwai masu sakashi yazomin da farashin kud'i masu tsoka akan camera d'in amma nayi kunnen uwar shegu dasu, hakanne yasakasu k'ok'arin salwantar da rayuwata wai tunda Na hanasu camera, nasan sunajin tsorone saboda Na kusantu da Galadima a lokacin, zan kuma iya bashi camera d'in, saidai abinda basu ma saniba tuni Camera d'in tabar hannuna. Alhaji Halluru abokinane Dan school mate d'inane, ada babu wata alak'a mai k'arfin tsakanina dashi, amma daga baya sai yayta Jana a jikinsa, ban fahimci manufarsaba dagashi har Alhaji Mamman, Dan da zuciya d'aya ni nake zaune dasu. Sai wannan karon da suka tabbatarmin da zulwa jahainin fuskarsu, sannan suka tursasa y'ay'ana biyu Dana d'auka nabama y'ay'ana Alhaji Halluru aure saboda yarda wai su d'akko musu camera a d'akina kosu kashesu dani dakuma iyayensu mata, sun razanasu da cewar sun dasa bomb a gidana, agabana duk suka sanar musu a waya. Abinda yasa ban damuba nasan k'arya suke, sannan Camera d'inma bata gidan, duk k'ok'arin lalatama Galadima sirrika da sukayi agabana sukayishi, amma ALLAH baibasu nasaraba, jin asirinsu zai Toni ta hanyar Garkuwa da y'ay'ansu da Galadima yayi shine suka shak'amin abinda ban saniba, daganan ban kuma Sanin ina kaina yakeba sai a asibiti yamai shari'a”. Wannan bayanima Na Abba ya girgiza zukata sosai. Dan har alk'ali kasa motsawa yayi, saidai yaja kusan mintuna biyu sannan ya sauke ajiyar zuciya mai k'arfi. Ya buk'aci a kawo masa camera nanda awa 2 kacal. Anbar lokacin a matsayin hutun kotu. Babu Wanda yaso matsawa konan da can, kowa burinsa dai camera ta iso aga mita k'unsa. Galadima ya kira Munaya, yace ta shirya ga Sarkin motanan zasuzo da Nuren su kaita masarauta ta duba cikin gifts d'inta Na Aure data samu Abba yace camera Na ciki. Dayake a labarai an nuna takuma gani, sai kuka dama takeyi da mamakin miyasama bata duba gifts d'in auren nataba tun wancan lokacin? Koda yake bata dad'eba a Nigeria suka wuce India, itakam a dukkan zaman da suka d'an tayi idan sun dawo bata sake bi takan gifts d'inba, to kawai tace masa ya yanke wayar, Dan yanzu babban burinsa kawai a tabbatar camera d'in tana wajen nata. Tana gama shiryawa sarkin mota yazo da Nuren dakuma police, bata d'auka yaro ko d'ayaba tafito suka tafi masarauta. Sun iske masarautar tsit, tamkar anyi sharar mutane, kowa Na sashensa abinda ke faruwa yama zukatansu murus, hannu kawai take iya d'agama hadiman sashen nasu dake gaisheta, basu damuba, dansunsan tana cikin wani yanayine. Sashen nasu yayi y'ar k'ura, saboda kwana uku babu kowa a ciki, Munaya kanta tsaye bedroom d'inta ta shige kawai, ta bud'e wardrobe nata tashiga fiddo gifts d'in aurenta data tara gefe, tareda Na haihuwar su Abdurraheem. d'ai-d'ai taita farkesu, idan taga bashi bane ko bud'awa batayi take jefawa saman gado, tasha wahala matuk'a kafin ta gano akwatin da idonta ya ta6a tozali dashi a d'akin Abba itada Munubiya, rungume akwatin tayi ta fashe da kuka maiban tausayi, ana haka kiran Galadima ya shigo wayarta, share hawayenta tayi ta d'aga. A d'arare yace, “kin hanshi?”. Cikin dariya da kuka ta amsa masa da eh ta gansa, shima murmusawa yayi, yace, “maza Ku tahoto, mintuna 46 suka rage a lokacin da alk'ali ya bada, sonake kawai a kammala shari'arnan a yau”. Munaya ta amsa da “to gamunan.................✍🏻 *_“insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu, koma mike cikin camera d'in dai zamu gani, nima Na k'osa nagani a wuce wajen😬🤦🏻‍♀”_*. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻a zuwa, saidai a dad'e ba'a zoba😏🐢. *_ALLAH ya gafartama mahaifanmu_*😭👏🏻 [8/3, 3:35 PM] +234 810 341 4063: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣6⃣ .................Jin tsayuwar motoci ya saka Ameer lek'awa ta window, juyowa yay ya kalli Galadima, “Ranka ya dad'e y'an sandane”. Baki Galadima ya ta6e, ya share tamkarma baijiba, yana cigaba da bud'e wasu file daya fiddo a briefcase. Saida yaja kusan 1 minute sannan ya mik'ama Nuren dake kusa dashi wasu files, ya zaro takarda kuma yay rubutun dabai Gaza layi biyarba ya mik'ama Ameer da wata k'amar waya a kwali. Kar6a Ameer yazo yayi, batareda Galadima yayi magana ba ya nuna masa window. Muftahu daya fahimta yace, “Ameer ka jefa musu takardan da wayan”. Ameer ya amsa da to, yanufi window d'in, cikin dabara ya jefa kwalin da takardar. Wani d'ansanda dayaga tahowarsu yay saurin zuwa kusada window d'in, ALLAH yabashi nasarar cafewa. D.p.o dake tsaye tare da sauran police ana shawarar yanda za'a shiga gidan ya kaimawa. Yay salute nasu kafin ya Isar da sak'on dukda yasan duk sunga daga ina kayan suka fito, d.p.o ya gyara tsayuwarsa yana fad'in “bud'e kwalin mu gani”. Bud'ewa yayi, yaciro wayar yana cewa, “wayace sir”. Cikin ta6e baki d.p.o ya jinjina kansa, yace, “takardar fa?”. Itama bud'ewa yayi, yafara karanto abinda ke jiki, wanda Galadima ya rubuta da harshen nasara. *_Kamar yanda suka fad'a Muhammad Sameer ba d'an ta'adda baneba, inhar zakubi yanda nace lallai yarannan zasu fita lafiya, idan kuma har kuka nuna k'arfin iko, zanta jeho muku gawarsu d'aya bayan d'aya ta saman benenan, ga wayanan, idan kuna buk'atar magana koni ina buk'ata ta wadatar, Dan kar wani yay gigin cewa zai shigo. Idan nayi ba dai-daiba a gafarceni👏🏻_* Daga d.p.o har jama'ar dake kusa dashi duk ajiyar zuciya suka sauke, ya jinjina kai yana cije bakin mamaki, cikin sauke numfashi yace, “saimu bishi yanda yakeso mugani, idan munga zai mana wasa da hankali sai a d'auki mataki, C.. babangida a zagaye gidan”. “Ok sir”. C babangida ya amsa yana salute nashi. Dandanan suka warware wani blue d'in zare suka zagaye gidan dashi, mutanen anguwa dasuka fara fahimta harsun fara taruwa kallo, harma wad'anda sukaji a labaran sunfara gangarowa anguwar damin ganema idonsu. Duk abinda ke faruwa Galadima Na zaune k'afa d'aya kan d'aya yana kallo ta CCTV, sai famar buga pen yake saman la66ansa a hankali, suma dai su Muftahu dasu Harun suna kallon komai. Kujera aka kawoma d.p.o ya zauna, dayake da sauran safiya babu maganar neman runfa ko umbrella. Wayar d.p.o ya kar6a da kansa, dan case ne Na manya IG da kansa yakirashi, yakuma abbatar masa shima yana nan zuwa. Shiru d.p.o yay yana bincikar wayar da Galadima ya aiko da ita, babu komai a cikinta sai Number guda d'aya, baice komaiba yaciro wayarsa yayma IG bayanin komai. Daga can IG yafara fad'a, wai tayaya zasu saurareshi, bayan d'an ta addane, duk Wanda zai iya kidnapping aiko d'an ta'addane, kawai su nuna masa k'arfin iko wajen ku6tar da yaran. Shidai d.p.o ya kwantar da murya cikin sigar lallashi yace, “Nidai Sir da ace za'abi ta tawa daminbishi a hankali, maybe akwai sak'on da yakeson isarwa, karfa mu manta shima d'an manyan mutanene, shikansa akwai sarauta mai daraja a kansa, ai mai martaba bazai ta6a jin dad'iba shima, tunda ya buk'aci dama mu bashi, idan munga batai manaba saimu d'auki mataki”. IG yace, “shikenan, Ku kirashi muji miyake buk'ata, nima a had'a dukkan maganar da zakuyi dani naji komai, dukda munama hanyar isowa yanzunan”. Cikeda farin ciki d.p.o yace, “ok sir”. Duk kayan aikin dasuke buk'ata suma sun tanadesu, yayinda y'an jarida suka fara isowa wajen. Shima C.P ma saigashi ya iso, duk suka k'ame wajen salute nashi har d.p.o. Ya amsa musu cikin jinjina kai, sannan ya buk'aci jin mi'ake ciki?. Bayani d.p.o d'in yamasa, shima ya gamsu da shawarar abi komai a sannu d'in. Galadima ya murmusa yana lumshe idanunsa yana sauke ajiyar zuciya. Saboda dukkan wayar da d.p.o yay da IG a kunensa ne. Sudai su Nuren sunyi jugum-jugum Dan son ganin minene shirin Galadima waine?, da har yaza6i fiddo kansa wa duniya a matsayin mai laifi?. Kiran da C.P yayi da kansane ya shigo wayar Galadima bud'e ido yayi yana kallon su ta CCTV, sannan yay picking call d'in, shiru yay yak'i magana, saida C.P ya fara masa sallama sannan ya amsa. C.P yace, “Ranka ya dad'e barka da safiya”. Baki Galadima ya ta6e, ya amsa da “Barka dai”. Gyara zama C.P yay yana kallon saman gidan, duk su Galadima suna ganinsa, yace, “Ranka ya dad'e muna saurarenka, ka fad'i buk'atar taka, inhar batafi k'arfinmu ba za'a biya maka insha ALLAH ”. “Humm” Galadima ya fad'a yana mik'ewa tsaye, duka hannunsa Na zube cikin aljihu, dayake yana amsa call d'in ne da abin da ke kunnen sa. Falon ya shiga zagayewa cikin takunnan nasa na k'asaita da izza, saikace namijin tantabara yana gwada gasar tafiya a gaban matarsa😜🤣. Suko sai binsa da kallo suke tamkar wani magiji. A hankali yace, “Buk'atata ta farko shine iyayen yarannan su fiddo Alhaji Auwal fharuk, idan sunyi haka lallai zakuji manufata kai tsaye batare dana ja muku raiba, Dan nima ina buk'atar hutu”. C.P ya shiga jinjina kansa kawai yana sauraren Galadima da dukkan sauran police d'in dasuma sukeda alhakin jin komai ta hanyar abinda suka saka a kunne. Bai k'ara komaiba ya yanke wayar, Yakoma mazauninsa ya zauna yana kallon yaran dasuma dukshi suke kallo, d'an murmusawa yayi yana d'aukar ruwan daya ajiye, saida ya bud'e murfin ya mik'ama Wanda yake kusa dashi. Shima yay murmushi yana girgiza kai da fad'in “A'a ranka ya dad'e, Na gode”. Galadima ya mik'ama sauran suma, amma duk sai sukace A'a, murmushi yayi yasaka kayansa a Baki yasha, yana kallon Harun daya zuba masa ido, rabi yasha ya mik'ama Harun sauran, amma saiya kauda kansa gefe, Galadima ya ta6e baki yana d'aga kafad'a alamar kaika Sani. Sauran ruwan ya ajiye yana kuma kallon yaran, da hannu yakuma yima Na farko alamar yaya sunansa?. Bai fahimtaba Dan haka ya kalli Na kusa dashi, sannan yakuma kallon Galadima yana nuna kansa da fad'in “Sunana wai?”. Galadima ya jinjina kai yana lumshe idanu. “Sunana Ahmad Bana bb gana". Galadima ya had'e yatsansa babba da manuniya👌🏻 alamar nice name. Ahmad yace, “Thanks you sir”. Na kusa dashi Galadima ya sake nunawa, shikuma yace, “Ahakam Balala”. Shima jinjina Galadima ya masa, nakusa dashi kuma Gebirel Timothy, sai Nerh-nerh Bilkisu Mansur, Rahma Abdul-naseer, Yassar Mamman, Sulaiman sager sulaiman, Marcel Miracle. Cikin murmushi Galadima yace, “Duk sunan y'an gayune daku”. Gaba d'aya suka sanya dariya, banda Harun da Alhaji Darma, Harun yasan Galadima sosai, dama yanada tsokana idan yaso hakan, koda kai zakayi dariyar shi ya fuske kuwa. Galadima Yakuma fad'in “Duk kun kammala Secondary schools ne?”. Duk suka amsa da eh, kowa yashiga fad'a masa matsayin karatunsa da abinda suke karanta, dukda ba magana yakeba murmushinsa Na sakasu farin ciki..... .............★ A can kuwa waje, police nata k'ullawa da kwancewa da jiran isowar IG, Dan yace su jirayi zuwansa. Dukda Galadima yana hira da yaran hankalinsa nakan saurarensu ta abinda ke kunnensa. Babu dad'ewa saiga IG ya iso, kar6ar wayar yayi da kansa bayan sungama salute nashi ya zauna, ya kuma kiran Galadima da kansa. Galadima yay picking amma sai yak'i magana yanzunma, hakanne yasaka IG yin magana cikin takaici da fusata, “Kai bamason rainin hankali, kafad'i abinda kawai kakeso duka amaka kabasu yaransu”. K'ala Galadima bai ceba ya yanke wayar. Mamaki ya kama IG, C.P yace, “Sir dadai anyi hak'uri an musu magana kawai suma aji mizasu ce”. Cikin matuk'ar takaici IG ya dangwarar da wayar yana huci da cire hular kansa, da hannu yayma C.P umarnin a kirasun. Da Sauri Aka danna kiran wayar d'aya daga cikin su, dama duksun tattarune a waje d'aya, Dan haka ya saka Hans free duk sunaji. C.P da kansa ya sanar musu buk'atar Galadima, kallon kallo aka dungayi, kowa ya kasa magana, Shidai C.P ya yanke wayar yana fad'in “nanda mintuna 10 zasu kira”. Suna ganin C.P ya yanke wayar suka hau cecekuce da fad'in yaronan yagama raina musu hankali, kaza-kaza dai, wasu suna bada goyon bayan abadashi sai abi tawata hanyar a kar6i camera d'in saboda suna matuk'ar k'aunar yaransu, wasu kuma sunce kar'a sakeshi, Dan haka tamkar tonon sililine agaresu. Sundai kasa samun matsaya har 10minute's ta cika C.P ya sake kira. Ba'a samu Wanda ya iya d'agawaba harta yanke....... (**************************) Zuwa yanzu gidan su Munaya sunsan halin da'ake ciki game da Galadima dakuma maganar fitowar Abba, Dan y'an jarida nata yad'a komai live a gidajen redio da TV, ga masu d'auka a waya y'an gani da ido dasukazo suka kafa suka kuma tsare. Kuka dai Munaya Na shansa, tayi wujigi-wujigi, miji da Uba duk suna cikin matsala, da k'yar inna ta bata tea tasha da kanta, yaranma sai an mata dole take shayar dasu, ta lafe jikin innarsu tanata hawaye daga ita har Munubiya, yaran sai innaro dasu mama rabi'a da sukazo gidan Tun farar safiya ke kula dasu. A can gefe kuma Zarah da Siyama NATA zagayen d'akin Abba Dan son samun damar shigewa su d'auki camera🤦🏻‍♀. ************************** Alhaji Hallurune yabasu shawarar su d'auka kawai suce su k'arya ake musu Alhaji Auwal baya hannunsu. Wannan shawarar sukabi, da Kansu suka kira C.P suka shaida masa. Sharri Galadima ke musu. Galadima dakejin komai yayi murmushi kawai yana cizar lips. Laptop d'insa ya janyo yafara danne-danne. Daga can C.P ya yanke wayar yana Neman izinin IG domin kiran Galadima shima. IG ya bada izini zuciyarsa Na sakejin zafin Galadima da rainin wayonsa. Saida ta kusa tsinkewa sannan Galadima yay picking, C.P ya sanar dashi amsar da suka bada. Cikin murmushi mai sauti da har su C.P sukeji Galadima yace, “ga za6i biyunan, kodai su fad'i inda yake, kokuma su sakoshi, kokuma shi yasaki video d'in yanda suka saceshi”. Jikin C.P fa kansa yafara sanyi, Dan yafara hango k'amshin gaskiyar Galadima. Bindiga Galadima ya nuna Alhaji Darma da ita, yamasa alamar ya matso gabansa, jikin Alhaji Darma Na rawa ya matso, waya ya mik'a masa, sannan ya danna kiran su C.P yana fad'in a had'ashi dasu yanzunan. Kallon IG C.P yayi, alamar neman izini, IG ya bada damar hakan. Dan danan aka had'a Galadima da su, bindigar hannunsa ya d'ora saman kan Ahmad, maimakon Alhaji Darma, jikin Ahmad yafara rawa, tuni yafara kuka saboda tsoro, tsawa Suka dakama Galadima daga can. Ahmad daketa mazari ya sanya kuka yana fad'in “Dady please and please kubashi abinda yakeso Dan ALLAH, wlhy zai kasheni, wayyo daddy I love you so much”. Tuni Alhaji Bana ya rikice jin muryar d'ansa, Galadima ya cire bindigar daga kan Ahmad ya harbata gefe, k'arar ta tsorata su Ahamad suka rikice da ihu. Rud'ewa su Alhaji Bana sukayi, Dan azatonsu Galadima ya kashe Ahmad ne, su kansa su IG dake waje duk sun tsorata da tunanin ko Galadima ya harbi wanine a cikinsu. Galadima yace, “idan Baku shirya sakinshiba zan kashe Na gaba kuma”. A tare suka hau ihu kowa yana rige-rigen fad'in zasu saki Abba. Galadima ya ta6e baki yana gimtse kiran. Alhaji Bana dai ya suma tuni, saboda tunanin an kashe masa d'a. Saidai suka zuba masa ruwa ya farfad'o, kuka rurus yashiga musu yana kiran sunan Ahmad d'insa, Yakuma rikicewa lokacinda Hajiya Fannah Maman Ahmad ta kirashi. Kasa d'agawa yayi....... **** Galadima yay kiran su IG yana fad'in “inhar suka nakasa Abba ko kawoshi da wani mummunan raune abakin ran d'aya daga cikin y'ay'ansu, Dan haka a matsayinsu Na police su gargad'esu. ********* Antura Police inda suka kwatanta aje a d'akko Abbansu Munaya. A inda aka d'aukeshi suka iskeshi ajiye cikin mota a sume, haka suka d'akkoshi suka taho, kai tsaye asibiti aka wuce dashi domin duba lafiyarsa, dukda babu wani ciwo a jikinsa Na alamar duka sai fashewar baki da kumburin da fuskarta tayi shima bada wani yawa can sosaiba. Galadima sunga komai a TV saboda nunawar da akeyi, hawayen da suka taho masa ya had'iye da k'yar yana sunkuyar dakai danma kar wani cikin yaran kosu Muftahu su fahimci wani Abu, saidai tuni Nuren and Muftahu da Harun sun fahimceshi, Dan sunsa halayyarsa duka, yana da tausayi ainun. Ran Harun A 6ace yake akan bada Abba dasu Alhaji Mansur sukayi, zuciyarsa sai tafarfasa takeyi, gashi kuma a d'aure. Galadima ya mik'e yana bada izinin kowa yaje yay alwala time d'in salla yayi. Idan kuma anyi salla su Farhat su shiga kitchen nema musu abinci. Wannan adalci Na Galadima yanata tasiri a zukatan yaran, harsu gebiral. Duk yanda Galadima yace haka sukayi, har Harun dake d'aure saida aka kwanceshi bisa tsayawar Ameer kansa da bindiga yay alwala. Koda su IG suka nemi yin magana da Galadima saiya jefa musu takardar yana sanar musu time d'in salla yayi, bazai sake saurarensuba sai yayi salla.. Dole sukabi yanda yakeso, suma kuma ya tunatar dasu abinda suka manta. .............................★ Bayan idar da salla da gama girkin su Farhat aka kawo abincin kowa ya d'ebi iya buk'atarsa, yanzuma Galadima bai Ciba, kwanciyarsama yayi cikin kujera ya lumshe ido. Harun dai anji wahala anci yanzu🤣😜. .............................★ Tuni mazan gidan su Munaya suka d'unguma zuwa asibitin Dan duba halin da Abba yake ciki, matan dai da yaran an barsu a gida, sai innaro kawai data Dage sai taje aka tafi da ita. .............................★ Buk'ata ta biyu da Galadima ya kawo bayan idar da salla itace a tura jami'an tsaro suje subama iyalan Abba tsaro a gidansa, hakama a asibiti. Babu musu IG yasaka C.P, shikuma CP yabama D.P.O Umarni, dandanan aka sanar da station d'in yankin su Munaya, aka kuma k'ara dawasu police d'in harda mata da zasu shiga cikin gida. Munaya taji dad'in hakan da Galadima yayi, Dan a tsorace tale dama. Dole kuma Zarah da Siyama suka nutsu, Dan Munaya k'ofar Abba taja zugar y'an uwanta suka shimfid'a tabarma sukayi zaman jugum-jugum d'in a can.🤨👍🏻. ************************ A masarautar gagara badau kam babu abinda kakeji Na tashi sai k'ananun magana. Bayi da kuyangi, dogarai da y'an gidan, manya da yara, kowane hadimi burinsa yafara kaima sashen dayake gulma, sunyi gungu-gungu suna tayi, sai anga wani babba zai wuce saikiga an watse. Mai martaba ya kira papi, dukda yasan shima yaga komai, bayan sun gaisa a mutunce irin gaisuwar d'a da uba, suka shiga tattauna abinda ke faruwa, papi yace, ya kirashi amma wayarsa a kashe, yakira Nuren ma shima waya a kashe, Dan yasan lallai a tare suke shuka wannan tsiyar. Mai martaba yace, “To amma Abba kaga kuma yanzu ga surukin namu sun fiddo kamar yanda ya buk'ata. Ina ganin akwai wani Abu da Sameer keson ankarar da jama'a Wanda mu bamu San dashiba, nasan halin yaronnan yanada k'yawawan halaye ababen koyi......”. Cikeda 6acin rai papi ya katse mai martaba, “Jalaludden komai k'yawun halin Muhammad a yanzu ba kowane zai gansu koya yarda dasuba, dukda inaji ajikina bawai ganganci ya sakashi yin hakanba, dama yanada hujja, amma miyakai Na kisa?, a labarai sun nuna ya kashe yaron Alhaji Bana, shin wannan halin mutanen kwaraine? Wannan hanyar dayabi fa bazata ta6a 6ullewa da shiba sai 6ata masa suna damu kanmu, daga fitowar maganarnan zuwa yanzu nasamu kira babu adadi”. Mai martaba yace, “kayi hak'uri Abba. Insha ALLAH zan shirya naje wajen zuwa anjima kad'an”. “Shikenan. Idan naga nima abin yayi tsamari zan taho”. Sallama sukayi kowa yana jimami akan lamarin. Tunda labari yakaima mama Fulani tashiga tafa hannu tana sallallami da fad'in “A lallai zai iya zai aika, yo wannan yaron mai ido a tsakar goshi, fitinanne zai 6atama masarautarmu suna akan wani banzan talakan surukinsa, akuwa yanda ya kashe d'an mutane shima kasheshi za'ayi, idan munan ya rainamu yanzu kam ya d'ebo ruwan dafa kansa, fand'ararre kawai gagararre”. Haka taita k'ananan magana da jifan Galadima da munana. Oho shi baimasan tanayiba☹😏. ******************** A asibiti likitoci sun Shiga bama Abba taimakon gaggawa, Dan ba'asan minene ya sumar da shiba, tunda babu wani alamar duka ko harbi ko makamancin wannan a jikinsa.. ************** Suma police sun buk'aci Galadima ya basu gawar Ahmad. Murmushi yay yana kallon Ahmad d'in dake zaune yana shan ruwa saboda tsoratar dayayi sosai ta harbin da Galadima yayi, har yanzu yakasa sakin jikinsa, salla ma da sukayi a d'arare yayita, yazata da gaske shid'in aka harba, saida Galadima yayma Saleem nunin abashi ruwa, Saleem yakawo ma Ahmad ruwa, a lokacinne ya farga da Ashe yanada rai bai mutuba🤣😜. Ya kar6i ruwa kuwa jiki Na rawa ya shiga kwankwad'a idonsa akan Galadima dake masa murmushi, yana bama su IG amsa da fad'in “karku damu yalla6ai. Inada freight d'in dazan dunga saka gawarsu anan, bayan aiki ya kammala saisu d'auki y'ay'ansu sumusu sutura, idan kuma sunyi abinda nakeso kaga magana ta k'are, gawar Ahmad kawai ce a k'asa dai yanzun, sai idan ank'imin yanda nakesone za'a samu fiye da hakan dai”. C.P ya jinjina kai yana gyara tsayuwa, idonsa nakan ginin, yace, “to miye buk'atarka ta gaba yanzu?, tunda gashi an maka ta farko ai”. “Eh tabbas anmin, dukda dai ankawoshi ba'yanda Na soba”. “amma ranka ya dad'e suma ai ankashe musu yaro d'aya”. Gira Galadima ya shafa da d'an yatsa yana ta6e baki, “ito dakuma wannan Dan wannan fa, yanzu dai inaga buk'atata tagaba shine ku kama mutanen nan guda 11 dazan lissafo”. “Muna saurarenka, dawa-dawa?”. Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, cikin Nisawa ya gyara zamansa yana d'aukar takardar dake gabansa ya shiga lissafosu. “Alhaji Balala, Alhaji Bana baba gana, Alhaji Abdul-Naseer Nafi'u, William Solomon, Hajiya A'i Barnawa, Alhaji Sageer Sulaima Sulaiman, madam Victoria, Mansur Habibu Abu, Josaya bamma, Alhaji Mamman k'afur, Alhaji Halliru garba”. Kallon kallo aka tsayayi tsakanin IG da sauran police, sai C.P ne yasamu k'arfin halin cewa “amma to Ranka ya dad'e akan wane dalili? Kasan dai bazai yuwu muje kama mutane babu dalilin komai damuka saniba”. Wani muskilin murmushi Galadima yayi, ya kwantar da kansa jikin kujera yana lumshe ido da cije lips, “Dalilin ai a fili yake yalla6ai namu, bisa dalilin Samun Alhaji Auwal Fharuk a hannunsu mana, dan yakamata asan dalilin samunshi a hannunsu, miya musu? Mi suke nema a wajensa? Baniba nasan dukan jama'ar garima abinda sukeson ji kenan, kunsan dai bazan ajiye ayukan gabana da jiyyar mahaifina nazo Nigeria Na zauna Ina kama yaran mutane saboda rashin aikinyiba ai, aimin kokuma nakuma aika yaronsu biyu barzahu yanzunnan!!”. Galadima ya k'are maganar cikin tsawa da matsanancin fushi. Tsawarsa saida ta kad'a hanjin yaran, hatta da Harun dasu Muftahu saida suka rumtse ido, suma haka police d'in dake sauraren Galadima. IG ya mik'e daga zaunen dayake yashiga safa da marwa Na mamakin wannan lamari, sukan ai ansakasu a tsaka mai wuya, cikin tsakkiyar fad'an manya. C.P ya kira suka koma gefe suna tattaunawa. ............................★ A can kuwa hankalin su Alhaji Sageer ya kuma k'ololuwar tashi, Alhaji Mamman yace, “lallai yaronnan anyi tsinanne, dama wannan ranar Na ringa gudu tun boss nada rai (tanderu yake nufi), amma wasunmu sukace yaron bai Isa mana komaiba, gashinan rana tsaka yana Neman zame mana RAINA KAMA....” “Yama zama ai, Dan gayya kawai muka fara gani yanzun”. ‘Hajia A'i ta fad'a a tsorace’. Duk sun kasa zama waje d'aya, Miracle yace, “yanzu nan da mutuncinmu za'ace wai y'an sanda su kamamu a k'asarnan?, lallai yaronnan yataro March wlhy”. “Kokuma mune muka taro March d'inba”. Alhaji Bana dayake cikin kukan mutuwar d'ansa yafad'a yana share hawayen. ...............................★ IG sun yanke shwarar bin umarnin Galadima kawai, kodan tseratar da yaran, yad'anyi magana da manyan dake kusa dashi dukda shine Oga kwata-kwata, kowadai yabada goyon bayan a kamasun kawai. Dan haka IG da kansa yay kiransu, Yakuma basu dama a girmamame akan sukai Kansu kawai station d'in dake kusa dasu, kodan rayukan yaransu, daga baya za'asan abunyi insha ALLAH”. Galadima dake saurarensu a zuciyarsa yace, abinyi kuma ai saidai a prison. Duk sunk'i amincewa, wasunsuma sai bak'ak'en magana suke fad'a. waya Galadima ya jawo yana daddannawa, sannan yayma Marcel nuni yazo, Dan yaji babansa yafi kowa zak'ewa, jikin Marcel sai 6ari yakeyi, ahaka ya rarrafo gaban Galadima. Galadima yace, “'Dauka wayarka anan”. Jikin Marcel na rawa ya d'auka. “Kira daddynka”. Dandanan yay kiransa, bugu d'aya kuwa ya d'auka shima jiki yana 6ari, duk suma sukayi tsitt suna jiran mizaice. Galadima ya d'orama Marcel binduga a tsakkiyar kai, ya juya idanunsa alamar yay magana. Marcel ya sanya kuka saboda tsoro. Rikicewa daddynsa yayi yana tambayar mi aka masa? Badai yay musu komaiba ba ko?..... Katseshi Galadima yayi da fad'in “Zandai yimasa, Dan kaima yanzu d'anka zai wuce Inda Na Alhaji Bana yatafi”. “kai kai dakata please ka dakata, nidai Na yarda zan mik'a wuya, karka ta6amin yaro kaji Na rok'eka”. Cire bindigar Galadima yay yana maida kunamar da fad'in “shawara mai k'yau, lallai kanason d'ankan nan, ka tambayi abokanka, Wanda bazai mik'a wuyanba saiya fad'a yanzun nan”. “karka ta6a mana yara please, duk zamu mik'a wuya”. Galadima ya tuntsire da dariyar da wanima zai iya rantsewa bai ta6a ganin yayiba, yace, OK, good dattijan k'asa, saina jiku acan”. 🤣🤣ana shagali a Nigeria yau kam🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀ amma Nigeria novel ba tamuba😜. Su Alhaji balala dai kam sun mik'a wuya, da Kansu suka kai Kansu police station mafi kusa, daga can suma d'aukesu zuwa inda IG yace. Galadima yay hamdala ga ubangiji dukda bawai komai yagama kammaluwa bane, amma lallai an d'akko hanya. Ya bada Umarnin tashi suyi sallar La'asar, kafin a dawo a cigaba da gashi😜. ....................................★ Bayan sun idar da salla C.P ya kira Galadima, suka shaida masa su Alhaji Bana suna hannunsu yanzu haka. Galadima dake tsaye yace, “Alhmdllh, zuwa safiyar gobe kuma sai a kai case d'inmu Court, Dan inason komai yafarune cikin gaggawa ya k'are, bana son jan jiki a aiki”. C.P ya kalli IG Dan jiran amsa. Kai IG ya jinjina masa alamar za'ayi hakan. C.P ya shaidama Galadima amsar IG. Galadima yace, shikenan, shi yatashi daga aiki, saikuma safiyar gobe. C.P zaiyi magana I.G ya dakatar dashi alamar ya barsa kawai. Ta6e baki Galadima yayi yana yanke wayar, ya maida kallonsa gasu Muftahu da duk suna maidashi television, gira d'aya ya d'age musu, sukuma sukai masa jinjina👍🏻. Kauda idonsa yayi ya maida ga yaran, yace, “yaya akwai mai buk'atar wanka ko barci?”. Gaba d'aya suka amsa da duk suna buk'ata. Kallon Ameer da Saleem yayi yabada Umarni da ido. ..............................★ 'D'aya bayan d'aya suka dinga kaisu suna wanka, duk Wanda yagama sai abashi lemo, batare daya San miye acikiba saiya shanye, daga sha ko mintuna 3 basa k'arawa suke 6ingirewa barci🤣. 🤣🤣ho Galadiman mu kasan takan tsiya, Zuma kenan, ga zak'i ga harbi🤸🏻‍♀, kaga Na Munaya baban triplets, bada kanka a sare kaje gida kacema su mama Fulani an k'illesa👌🏻😜😂. Da akazo kan Harun k'in tankawa yayi, Dan haka Galadima yace su barshi kawai, amma harsu Malam Saminu da Alhaji Darma su Farhat duk sunma Kansu gyad'ar dogo sunje sun mik'e zasu huta. Nuren ya kalli Galadima cike da tausayi yace, “Brother kaima kad'anje ka huta mana”. Murmushin gefen baki Galadima yayi, yajawo lap-top gabansa yana girgizama Nuren kai alamar a'a.................✍🏻 *_ALLAH ka gafartama Iyayenmu_*😭👏🏻 [8/3, 3:38 PM] +234 813 221 4515: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ___________________ *_Na gaisheku, gaisuwa irinta musamman d'innan. Makaranta buk d'in RAINA KAMA dake JAMI'AR KUST dake WUDIL, alkairin ALLAH yakai agareku, ALLAH ya yalwataku da ilimi mai tarin albarka damu baki d'aya._* Ina inyinku irin Trillion's d'innan my guys🤸🏻‍♀😘😘😘😘❤❤. ____________________ *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣7⃣ ...................Abin surutu lallai ya samu, mak'iyan Galadima kuwa duk sun kasance a tsorace, Dan ba kowane ya fahimci inda shirinsa ya dosaba, hakama a cikin masoyan nasa, wasu suna ganin daidainsa wasu kuskurensa, kowa da irin fahimtar dai da yayma lamarin. Yauma dai haka suka kwana zagaye da police. Amma su IG duk sun tafi, d.p.o ne kawai tare da tawagarsa, kamar kuma yanda ya buk'ata sunakan tattara case d'in zuwa Court. 6angaren su Baffi kuwa lauyan Abie dukkan shirye-shiryen shiga Court suma suna akanyi. Dan dukkan shirin Galadima yasan dashi tsaf, hakan yasa koda yagani baiyi mamakiba, kisan Ahmad daine da akace yayi yabashi mamaki, dukda zuciyarsa bata aminta Galadima zai iya kashe yaro ko d'ayaba. Amma lallai hakan ya sakashi a rud'ani, harma ya kira sir Isa sukayi maganar. Sir Isa yace shima yagani a labarai amma gaskiya bai yardaba, akwai dai abinda duk basu saniba, Dan Galadima bazai aikata hakanba. Da wannan maganar ne Baffi yad'an samu Nutsuwa yacigaba da tattara bayannsa daduk abinda zasu kafa hujja dashi a court. Duk abinda ke faruwa Momma tasan komai. Dan Galadima ya sanar mata, baya kuma 6oye mata dukkan shirinsa akan wannan case d'in dama, amma sai tayi lup tamkar batasan anaiba, koda labari yazo musu saita taya su Aunty Mimi rud'ewar itama, harda pretending d'in kukanta tana Neman number Galadima, amma sai tak'i wucewa. Daga Baffi har mai martaba babu Wanda ya kirata akan batun, duk a nufinsu Na 6oyemata kar hankalinta ya tashi balle Na mahaifinsa dake kwance yana fama da kansa. Amma saiga kira daga mama Fulani, tafad'ama Momma maganar daduk yazo bakinta ta 6atanci akan Galadima, itadai momma cikanki batace da itaba, har tayi ta gama ta yanke wayar. Saiga gimbiya Zulfah ma ta kira Momma, itakam ai harda kukan makirci irinna y'an duniya. Itama dai tayi kid'anta tayi rawarta Momma Na saurarenta. Koda ta Yanke wayar saita kira munaya. Taita kwantar mata da hankali da lallashinta akan ta kwantar da hankalinta. Insha ALLAH komai zaizo k'arshe, kowace rayuwa takan tafine da jarabawa. Babu wani rai dazai rayu cikin farinciki da samun yanda yakeso 100%, dolene kowacce rayuwa akwai NATA k'alubale, nakowa kuma akwai ta hanyar dayake fuskantar nashi. Sosai Munaya ta gamsu da nasihar momma hakannema yad'an samu mata nutsuwa tad'an rintsa a wannan dare. .................................★ *_WASHE GARI_* Nasara ta farko da aka wayi GARI da ita shine farfad'owar Abba cikin hankalinsa, saidai har lokacin baya sanin Wanda yake a tare dashi, hakanne yasaka likitocin fad'in a k'ara masa lokaci yasamu isashen hutu. Ahalinsa sunsamu Kansu a farinciki ainun, hakama masoyansa, shikansa Galadima Yakuma samun kwarin gwiwa da karsashi akan aikinsa. An kuma shigar da case d'in Court kamar yanda Galadima ya buk'ata, abinka da lamarin manya har antsaida washe gari a matsayin ranar da za'a zauna Court d'in. Yinin ranar zubur Galadima baiyi magana da police ko d'ayaba, koda sun buk'aci magana dashi saiya had'asu da Muftahu ko Nuren. Daga k'arshe dai dolensu suna k'yaleshi. ★★★★★★★★ *_⚖RANAR SHIGA COURT_*⚖ Yau ta kasance ranar zaman court, shari'ar su Galadima Ce kuma farko da za'a fara saurara a court d'in, lallai wannan shari'a ta manyace, Dan court d'in ta cika da manyan k'asa wad'anda sunfi kud'i wahalar gani, amma yau gasu available, y'an jaridar ma manya-manya aka bari, k'ananun suna awaje sunyi tururuwa domin rajin nemawa d'an uwansu hak'insa wato Alhaji Auwal fharuk dayake a asibiti har yanzu cikin halin ni y'asu. Mukuwa talakawan gari y'an jiran jin yazata kaya mu sai dai gani a tv☹. Yo Wayaba asibi laya ubanta ba malam ba😬, ai ko babama da babansa aradu🤕. *_Court_* d'in tayi tsit babu abinda kakeji sai gudun fankoki da tarin manya jefi-jefi, dan babu alamun fara'a a fuskar kowa. Daga masarauta dai k'anin mai martaba ne yazo wato Garkuwa Hayatudden Abubakar, sai wasu daga tawagar y'an majalissar Sarki, harda waziri dayazo bisa tirsasawar mai martaba. Daga masarautar su Papi kuwa yarima mai jiran gado mahaifin su Nuren wato Wambai Abubakar Abdul-fatah Wanda yagaji sunan kakansu Galadima marigayi Abubakar kenan. Saikuma wasu daga jiga-jigan masarautar suma. Fitowar alk'alin alk'alai Othman Ibraheem gwannu tasaka dukkan jama'ar Court d'in mik'ewa domin girmamawa a garesa, (dan shima Alk'ali baba uban su babane shima🤭😝). Saida ya zauna sannan yabada izinin kowa ya zauna, Court d'in tayi tsit kowa ya Zubama alk'ali dake karanta takardar k'arar hankali kwance ido, kusan mintuna 3 ya d'ago yanabin Court d'in da jama'ar cikinta da kallo ta cikin eyeglasses nashi daya jawo k'asan ido, d'auke idonsa ya ya maida ga Lauyoyi dake zaune suna jiran kule, suce cas. Gyaran murya yayi yana maida idonsa ga takardar da fad'in “Ina wad'anda suke k'arar da kuma wad'anda akai k'ara? Idan kuma Lauyoyine to na masu k'ara da wad'anda ake k'ara suna inane?”. A tare Baffi suka mik'e shida abokan aikinsa su uku, cikin girmamawa ga alk'ali ya risinar dakai yana mik'a gaisuwa da fad'in “yamai girma mai shari'a sunana Barrister Usman Audu Tsanyawa, nine lauya mai kare Wanda yake k'ara, tare dani akwai Yohan Emanuel, da Bilkisa Ibraheem Musa (kutu melesi su bilyn Abdul anzama lauyoyin novel🤸🏻‍♀😎🤣😜). Bilkisu da yohan suka risina alamar girmamawa. Alk'ali ya jinjina kai alamar gamsuwa, su Baffi suka zaune, lauyan wad'anda ake k'ara shima ya mik'e, ya rissina tamkar yanda Baffi yayi, sannan yace, “ya mai girma mai shari'a sunana Barrister Adam Sadiq Adam, nine lauya mai kare wad'anda ake k'ara, tare dani akwai Barrister Aliyu Sa'adu yaro”. Barrister Aliyu ma ya mik'a gaisuwa ga alk'ali sannan suka zauna. Alk'ali yabama Baffi damar tashi domin yin magana. ALLAH Sarki dattijon kwarai kenan, masu wahalar samu cikin k'asa a halin yanzu, ya gyara hularsu ta lauyeyi dake Kansa, tare da farin eyeglasses d'insa dan rayuwa taja, ijiya duk sun raunana, ya kalli jama'ar cikin Court d'in sannan ya dawo da kallonsa ga alk'ali, yace, “yamai girma mai shari'a! Kamar yanda kowa yasani Muhammad Sameer Saifuddin Abubakar (Galadima) shine yake Neman son sanin miya saka wad'annan mutanen 11 yin gamayya wajen kama surukinsa harsu wahal dashi? Bayan kuma shikeda alak'a dasu bawai surukinsa ba?”. Kai Alk'ali ya jinjina, cikin sauke numfashi yace, “Lauyan wanda ake k'ara gareka”. Barrister Adam Sadiq Adam ya mik'e shima yana fitowa fili, yayinda Baffi Yakoma ma zauninsa ya zauna, Brr Adam Sadiq Adam yace, “yamai girma mai shari'a wace irin tambayace ke fitowa daga bakin lauyan mai k'ara? Ai sune yakamata ayima tambayar minene dalilin shi Galadima Na kama yaran wad'annan mutane 11 yayi Garkuwa dasu yau tsawon kwana biyu? harma da kisan wani a cikin su......... A hanzarce Baffi ya d'aga hannu sama yana mik'e da fad'in “yamai shari'a tambaya akaima lauyan mai k'ara, amsa kuma yakamata ya bamu baya sakko tashi tambayarba”. Hannu Alk'ali ya d'agama Brr Adam Sadiq Adam, yace, “Brr Adam ka gyara, amsa muke buk'ata, kanada dama kaima kayi taka tambayar daga baya”. Brr Adam Sadiq Adam ya risinar dakai alamun ban hak'uri sannan ya gyara tsayuwarsa yana fad'in “Yamai girma mai shari'a akwai abinda ke hannun Alhaji Auwal Fharuk Wanda mallakin su wad'annan mutane 11 ne, shine sukeda buk'atar kar6a”. Baffi yamik'e yana fad'in “yamai girma mai shari'a ko zamu iya sanin minene wannan Abu da suke tuhumar Alhaji Auwal Fharuk akansa, dahar suka kasa mik'ashi ga sharia domin kar6a har sai sunbi ta hanyar nuna k'arfin ikonsu?”. Brr Adam Sadiq Adam yay shiru yakasa cewa uffan, dan ganin tun a tashin farko yana shirin zurmawa. Ganin yak'i cewa komai Baffi ya kuma cewa “ya mai girma mai shari'a idan baza'a samu amsaba ina buk'atar d'aya daga cikin y'an wad'annan tawaga domin ya amsamin tambayata idan shi Barrister bai saniba”. Alk'ali ya jinjina kai yana bada Umarnin tasowar d'aya daga cikin su Alhaji Mansur. Dukfa abinnan dake faruwa Galadima yana kallon komai kai tsaye ta Computer, danshi baizo Court d'inba, babu damar hakan, yana fitowa a gidan police kamashi zasuyi, wannan yasa tukan zaman Shari'a Alk'ali yabada wannan damar ta had'a video call d'in da Galadima zai iya ganin komai da za'ayi kamar yanda IG ya buk'ata bisa umarnin shi Galadima d'in, kamar yanda ya shard'anta ko amasa hakan koya jeho gawar yaro d'aya ko yarinya. Hakan yasa sukai masa babu gardama. Alhaji Abdul-Naseer dake farkone ya taso, ya shiga inda aka tanada domin buk'atar hakan, ya fad'i sunansa da matsayinsa, sannan Alk'ali yabama Baffi damar masa tambayar. Baffi ya k'arasa jikin katakon d'aya shiga tsakaninsa da Alhaji Abdul-Naseer, idonsa a kansa yace, “Alhaji Abdul-Naseer, nasan kana d'aya daga cikin y'an wad'annan tawaga, shin kozaka iya amsa mana tambayar da lauyanku ya kasa?”. Murmushin Alhaji Abdul-Naseer yayi, cikin kwarin gwiwa yace, “Brr Usman, a ganina wannan sirrinmu ne, koma mi muke buk'ata a hannun Alhaji Auwal Fharuk mukeda alak'a dashi ai ba kowaba ko?”. Baffi yashiga jinjina kai yana murmushi, yayi taku d'aya biyu saikuma ya juyo ga Alhaji Abdul-Naseer, yace, “lallai wannan gaskiyane Alhaji Abdul saidai kuma dalilin sanin Court yanada alak'a da samo Alhaji Auwal Fharuk a hannunku, wanda ta silar kama y'ay'anku da surukinsa yayine kowa yasan hakan, saikuma gashi shi wannan bawan ALLAH Alhaji Auwal Fharuk a jiya daya farfad'o dukda baya cikin hayyacinsa, amma yana ambatar sunan Alhaji Halluru da jaddada lallai koda zaku kasheshi bazai bada wannan camera ba, domin shekarunma da kuka d'auka kuna ma rayuwarsa barazana bai bakuba balle kuma yanzu da lokacin Isar da ita ga Wanda akace ya Isar yayi, kenan Alhaji Auwal Fharuk k'arya yayi?”. Da sauri Brr Adam Sadiq Adam ya mik'e yana fad'in “ya mai shari'a wannan ai tamkar titsiyene Brr kema Wanda ake zargi, dan babu yanda za'ai la'akari da mutumin da baya cikin hankalinsa kamar yanda ya fad'a.....”. Shima Baffi azamar dakatar dashi yayi, yace, “yamai girma mai shari'a Barrister Adam bashida hurumin yanke hukunci akan yanayin Alhaji Auwal, sai ya bari bayanin likitoci ya tabatar mana hakan”. Alk'ali yay gyaran Murya da buk'atar ganin likitan dake kula da Alhaji Auwal Fharuk (Abba). Cikin mintuna 3 saiga doctor ya shigo. An sakashi d'ayan wajen, ya fad'i sunansa da aikinsa, sannan Alk'ali yace, “kaine likitan da ke duba lafiyar Alhaji Auwal Fharuk? ”. “eh nine yamai shari'a”. Alk'ali yace, “kozamu iya sanin wani Abu dangane da jikin Alhaji Auwal Fharuk? ”. “kwarai kuwa ya mai shari'a, an kawo mana Alhaji Auwal Fharuk cikin hali irinna suma, amma babu wani alamar duka ko harbi a jikinsa, saidai bincikenmu ya nuna an shak'a masa wani Abu. Daya saka numfashinsa Nisan zango, sai ajiyane bisa hukuncin ubangiji ya farfad'o, wad'annan kalamai sune abinda ya farka dasu a bakinsa, kuma kwakwalwarsa ras take, abinda aka shak'a masanne kawai bai sakesaba har yanzun, danma yanada jini mai k'arfine”. Cikin wad'anda suke zaune ma'aikatan Court d'in d'aya yaje ya kar6i wayar doctor da yay recording ya kaima alk'ali. Alk'ali ya kunna recording ya saurara, ya ajiye wayar gefe da sallamar doctor cikeda gamsuwar abinda yaji. Sannan shima yabada Umarnin sanin ita camera ta micece?. Baffi yakuma mik'ewa tsaye yana gyara k'atuwar rigarsa, yace, “ya mai shari'a, ita wannan Camera da wad'annan gamayyar mutane suke farautar rayuwar Alhaji Auwal Fharuk a kanta tanada alak'a da Muhammad Sameer Saifuddin Galadima ne, itace kuma musabbabin d'aukar yaran wad'annan mutane 11 dayayi yake tsare dasu a gida mai labba 67 dake anguwar tudun na ALLAH a tsakiyar binni, damin camera dai k'unshe take da abinda ya faru da tsohon Sarki dake jiyya a India, wato Mai martaba Saifuddin Abubakar tsawon shekaru 26 kenan ba'asan wad'anda suka aikata masa abinda ya kaisa da jiyyarba”. Turk'ashi, kallon kallo kenan, to lallai shine aka shigayi a wannan Court, nanfa k'ananun magana suka fara tashi tsakanin manya, Court ta harmutse da hayaniya babu maijin zancen wani, saida alk'ali ya tsawatar sannan akayi tsit. Inda kuma a gefe tsantsar rud'ani da rikita ta mamaye su Alhaji Balala, ko kad'an basuyi zaton shigowar wannan maganar da wuri ba cikin shari'ar, shima kansa lauyansu haka, tunda wawantar dasu Galadima yayi akan Shari'ar ta shafi d'aukar Alhaji Auwal Fharuk ne da farko. Alk'ali da shima kansa ya shiga wani yanayi ya buk'aci ganin Muhammad Sameer a Court. Baffi ya kuma mik'ewa yana fad'in “ya mai shari'a, ai Muhammad Sameer Saifuddin Galadima bashida ikon zuwa court a yanzu, domin kuwa yana can tsare da yaran wad'annan mutane 11 ne, kuma yana fitowa y'an sanda zasuyi ram da shine a matsayin mai laifi babbama kuwa, dan yanzu akwai laifin garkuwa da yara d'in a kansa, saidai munada hanya sassauk'a ta had'a wannan adalar kotu da Galadima kai tsaye”. Alk'ali ya bada damar hakan. Dandanan kuwa aka had'a Galadima da kotu, Wanda dama shi tuni yana ganin duk abinda sukeyi, sunedai basa ganinsa. Galadima dake zaune a falon gidan da yake tsare dasu harun ya mik'e tsaye domin girmamawa ga alk'ali, sannan ya gabatar da sunansa kamar haka, “ya mai shari'a sunana Muhammad Sameer Saifuddin Abubakar, ma'aikaci a hukumar bincike ta DSS”. Wani sabon kallon kallon aka koma, Wanda yaja hankalin mutane fiyema dana d'azun, hattada y'an masarautar gagara badau basusan da wannan aiki Na Galadima ba. Alk'ali ya kuma tsawatarwa, sannan ya maida hankalinsa ga Galadima yana fad'in “To Muhammad Sameer minene alak'arka da iyayen yaran dakake rik'e dasu, danmu ka rikita mana tunani, da farko kallon Criminal muke maka, saikuma gashi sunanka yafito a d'aya daga cikin manyan hukumominmu Na tsaro masu muhimmanci?”. Murmushi Galadima yayi yana gyara tsayuwa, ya hard'e hannayensa a k'irji yana sauke numfashi da cije lips, yace, “ya mai shari'a wannan labarine mai tsawo, amma tabbas abinda lauyana ya fad'a shine gaskiyar zance, Camera dake hannun Alhaji Auwal Fharuk itace babbar alak'ar dake tsakanina dasu, wadda nad'au tsawon shekaru akan nemanta, sai a shekararnan ne cikin watanni shida nasamu labarin inda take dukda banida tabbacin ita d'ince, bansan mike cikin camera d'inba, amma su Alhaji Balala duk sun Sani, tunda har suka iya salwantar da rayuka da yawa akanta, shi kansa Wanda suka hara a yanzu ALLAH ne kawai yasaka yanada tsawon rai, amma da tuni sun kasheshin, ni kaina rayuwata tasha hare-hare iri-iri harda jariran yarana da aka sace kwanaki 7 kacal da zuwansu duniya”. Alk'ali da yay shiru yana sauraren Galadima yaja dogon numfashi yana ta faman jinjina kai tamkar k'adangare yaga abinci mai manja😱🤭. Yace, “lallai wannan Court tana buk'atar jin cikakken bayani daga Muhammad Sameer Saifuddin, dan haka ta d'aga wannan k'ara zuwa nan da kwanaki uku masu zuwa, kotu tana bama y'an sanda Umarnin subar Muhammad Sameer Saifuddin ya fito daga wannan gida a ranar da Court zatayi zama Na gaba batare da koda masa hararaba, sannan kuma kotu ta bada Umarnin a cigaba da tsare su wad'annan mutane guda 11, likitoci kuma su cigaba da bama Alhaji Auwal Fharuk kulawa ta musamman dan shima kotu Na buk'atar ganinsa a zama Na gaba saboda son sanin mike cikin camera d'in”. Alk'ali ya buga gudumarsa yana mik'ewa. Gaba d'aya kowa ya mik'e har alk'ali ya shige. Galadima yay wani k'asaitaccen murmushi yana zaunawa cikin kujera bayan shigewar alk'ali. Muftahu, Nuren, dasu Harun dake zaune gefe suma suna kallon komai tun farkon Shari'ar duk sunyi mutuwar zaune tun lokacin da Galadima yafad'i kasancewarsa cikin hukumar C.I.D. Ameer ne kawai yay murmushi yana k'amewa da salute d'in Galadima. Shima baki sake su Nuren suka bishi da kallo suna nunashi alamar dama yasani shi?. Murmushi yay musu har hak'oransa Na bayyana ya had'e hannayensa waje d'aya alamar tuba a garesu. ★.....................................★ Yau kam Galadima wani farin ciki Na musamman ya tsinci kansa a ciki, ya shige d'akin da yake matsayin nasa a yanzu ya fad'a gadon yana rungume filo idonsa Na zirar da hawaye, ko a haka aka tsaya lallai yaci nasara, dan ya nunama su Alhaji Abdul-Naseer d'an zaki ya girma. Wayarsa dake saman gadon a can gefe yasa hannu ya janyo, ya kunnata, massages ne sukaita shigowa a jere-jere kamar jira, bai bud'e ko wanneba ya shiga binciko number Munaya, ya dad'e yana kallon Number amma ya kasa dialing, yaja wasu seconds kafin yatsansa ya sauka akan number ya danna kawai. Munaya Na zaune a falo tare da su Ayusher da kullum sai sunzo, d'an kunne ne ya shige cikin jikin Amaturrahman yanata cin jikinta basu saniba, sai yau da an ta6a fuskarta koyaya saita fashe da kuka, Munaya tarasa mike damun yarinya, dukta rikice ita kanta, saida laraba tace ta bata nono, tana kwantar da ita ta wajen kunnen sai takuma d'ad'ewa da kukan da Munaya ke jinsa har cikin jini, d'agota tayi tana duba wajen, Laraba tace, “Anya ba kunenta ke ciwoba?”. Munubiya dake kusada Munaya ta amshi Amaturrahman ta kifata a cinyarta tana dubawa, sai taga d'an kunne ne ya shige Ashe duk bayan kunnen yayi ruwa, tsoro ya kama Munubiya, cikin zaro ido waje tace, “innalillahi, d'an kunne natacin kunen yarinya bamu saniba”. Da an fara k'ok'arin ciremata saita kuma fashewa da kuka tana mimmik'ewa, gwaggo safiya data shigo yanzu saboda jiya ta iso akan abinda ya faru da Abba, ta k'araso cikin falon tana fad'in “mike faruwane?”. Bayani feena tai mata, gwaggo safiyya ta kar6i Amaturrahman tana cewar asamo mata ruwan d'umi da k'aramin handkerchief. Ana cikin hakane Galadima yayi kiran Munaya, tashitai tabar wajen tana had'iye kukan dake shirin taho mata saboda tausayin yarinyar. 'Dakinsu ta shiga, ta fad'a saman gadonsu ta kwanta tana amsa wayar. A hankali Galadima ya sauke ajiyar zuciya yana gyara kwanciya. Murya can k'asan mak'oshi yace, “babu fad'a miya kawo gaba yalla6iya?”. Murmushi Munaya tayi tana share hawayenta. Tace, “Kodai Kaine za'aima wannan tambayar?”. Jimm yayi saboda jin muryarta ba ayanda yasaniba. yace, “mike faruwa kike kuka?”. Mamaki ya kama Munaya, ta Yayama ya gane kukan take, cikin k'ok'arin kare kai tace, “ba kuka nakeba yalla6ai, ina yini”. bai amsa gaisuwarta ba yace, “kina wasa da sanin danai miki ko?”. Yay maganar cikin d'an kausasa murya. Munaya sai bataji dad'iba, tace “kayi hak'uri, dama Amaturrahman ce d'an kunne ya shigema a jiki taketa kuka, amma gashi can suna cire mata d'an kunnen”. Babu shiri Galadima ya tashi zaune yana fad'in “k ya akayi har d'an kunne ya ringa cin jikinta baki saniba? Anya kuwa kinason yarannan Munaya?”. Wani haushine ya kamata, tama rasa mizata Ce masa. Shima bai jira amsartaba yace, “maza ki tashi kuje asibiti a dubamin yarinya, karkuce zakuyi gangancin cire mata a gida wata matsalar ta biyo baya”. “Uhumm”. Kawai Munaya tace ta yanke wayar. Ta jefar da wayar gefe tana hawaye, shi kawai yaransane damuwarsa, harma zaice yafita sonsune dazai dinga jifanta da bata sonsu kulum-kullum, itafa wannan Abu yafara kaita bango wlhy. A can kuwa shima Galadima duk sai yaji ya damu, jiyake tamkar yay tsuntsuwa yafita yakai yarinyarsa asibiti da kansa, amma babu damar hakan. Ya dad'e jikin window tsaye yana kallon mutane daketa zirga-zirga a anguwa da police d'in dake zagaye da gidan har yanzu. Fita munaya tayi dan ganin ko ancire?, ta iske an cire ana gasa kunnen, Amaturrahman taci kuka harta koma ajiyar zuciya, Gwaggo Safiyya tace, “zoki zauna kibata tasha sai'a k'arasa gasawar”. Zuwa Munaya tayi ta zauna tana kar6ar Amaturrahman. K'in k'ar6ar nono tayi, sai ajiyar zuciya taketayi, Laraba tace, “yaranan zuciya irinta Magajin gari suke da ita, yanzu inba sa'a ba bazatashaba”. Dariya su Ayusher sukayi. Dak'yar dai Munaya ta turama Amaturrahman nono abaki ta kar6a. Akad'an kuma gasa kunnen dayay uwar huda naman wajen yafita sosai, k'ofar tazama babba. Munaya dake kallonta tasaka hannu tana goge mata zufar data taru mata a goshi, saikace wata babba. Galadima yanata kiran Munaya yaji kosun tafi asibitin amma bata d'agaba, dayake ta bar wayar a d'akinsu. Saida Ayusher taje d'akin ta gano, ta d'akko da sauri ta kawo mata tana saka mata a kunne. Maganarsa kawai munaya taji yana fad'an ina ta ajiye wayar. Ajiyar zuciya ta sauke tabashi hak'uri kawai, dan bata buk'atar jan maganar. Yace, “kunje asibitin?”. Munaya tace, “An cire mata ai, babu wata matsala tunda bai ta6a cikiba”. Ca yay ta d'auka hoton wajen ta turo masa yagani, kamar tace bazatayiba sai kawai ta cire wayar ta katse kiran, hoton wajen ta d'auka ta tura masa”. Tausayin yarinya ya kamashi ganin yanda wajen yay cinye sosai, Yakuma kiran Munaya yana jaddada mata karta sake akuma sakamata wani d'an kunne. To kawai ta amsa masa dashi dan a zauna lafiya. ..............................★ Tun daga ranar Munaya bata sake jin Galadima ba, saboda yayi busy da yawa akan shirye-shiryen shari'ar dake gabansu, dan fatanshi wannan zaman yazama zama Na k'arshe insha ALLAH. Alhmdllh jikin Abba anata samun haske sosai, dan sauk'i yana samuwa iya gwargwadon iko. *_RANAR DA ZA'A KOMA KOTU_*................✍🏻 Hummm😬 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭👏🏻_* [8/3, 3:39 PM] +234 813 221 4515: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣8⃣ .................Yauma dai kotun ba'a cewa komai, wad'anda ma basuzo zaman farkoba yau sunzo, Dan su sir Isa duk suna wajen da muk'arabansa, hakama tawagarsu Tanderu, Dan suma lauyansu a cewarsa yau yazo da sabon shiri, ranarma an mamesa ne kawai. Galadima yagama shirinsa tsaf cikin wani lallausan yadi sky blue dayasha d'inkin boda, Dan rigar iyakarta Rabin cinyarsa, kayan sunmasa k'yau matuk'a, danya fito ainahinsa Na jinin Hausa Fulani, ya Mirza hularsa sky blue itama, fuskarnan tayi fayau Dan hardasu gyaran fuska yayi abinsa, danma ya tabbatarma mak'iya yana cikin farinciki fiye da zatonsu, yana cikin saka sock's Nuren ya lek'o yana fad'in “Brother ka hanzartafa mun makara”. “umhum” kawai yace masa yacigaba da saka kayansa a tsanake kamar yanda yafara, danshi komai saurin dazaiyi akan Abu to anutse zaiyi abinnan, ganin haka sai kawai Nuren ya ida shigowa, ya durk'usa gabansa yana kama k'afar daya sakama sock's d'in ya saka masa takalmi. Baki Galadima ya tsa6e yana cewa, “kaifa shegen gaggawane dakai wlhy, ni bansan INA kuka kwaso halinnanba, haka Momma da Aunty Mimi suke, komai kunfison mutum yanayi kamar wani mazari”. Nuren ya sanya dariya yana saka masa d'aya takalmin, yace, “to sokake muke Abu kamar marasa laka a jiki? Munaya dai kam tana fama...” Hararsa yayi, hakanne ya hana Nuren k'arasawa, Galadima daya wani tsaresa da ido yace, “Tana fama da k'aniyarka”. Nuren ya mik'e yana fad'in “oho maka dai, mu ka fito su sarkin mota tuni sukazo”. Mik'ewa yay ya d'auki turarensa Na kullum a bag d'in daya had'o kaya ya fesa, k'amshin ya gauraye ko ina, waya d'aya ya zura a aljihu ya fito. Su Ahakam duk shagala sukayi da kallonsa, a ransu suna matuk'ar yaba tsarinsa, komai nasa abin birgewane, kamar yanda ya saba haka yabasu hannu da kansa sukayi musabaha dukda suna nok'ewa alamar jin kunya da girmamawa a gareshi, shikam babu ruwansa, inhar bakasan halinsa bane dolene tashin farko ka jefeshi da kalmar girman kai. Su Farhat ma suka gaisheshi cikin risinawa, wani miskilin murmushi yamusu yana d'aga musu hannu kawai, ya kalli Saleem tare da masa nuni yabama kowa kayansa. Saleem ya amsa da cewar “ok boss”. Bag d'in da wayoyinsu ke ciki ya d'akko, amma sai sukace sukam ya barsu, Dan inhar ba'a yanke hukunci ba zasu dawo su cigaba da zama dasu, Dan zama da Galadima akwai dad'i, kuma ko an yanke hukuncima masarauta zasu bishi. Shi dariyama abin ya bashi, hakanne yasakashi bubbuga kafad'ar Yassar dake kusa dashi yana sakin murmushin da har hakwaransa ke bayyana, ya wucesu yana sauka daga benen cikin takunsa Na birgewa. Suma duk binsa sukayi a baya, komai nasa Saleem ya tattaroshi, dan bazai sake dawowa gidanba koda ba'a yanke hukunci ba kuwa. Harun dai anyi laushi matuk'a, dan maganarma yanzu ba iyayin mai k'arfi yakeba, saboda saiya gadama yakecin abinci, babu kuma mai sakashi dole yaci. Cikar k'ofar gidan tabama Galadima mamaki matuk'a, yakuma d'aure fuska tamkar bai ta6a dariya ba, musamman yanda duk aka zubo masa ido, a Bayama an kallesa balle yanzu da yayi abun kallon, y'an sanda da dogaransa da suka zo d'aukarsa tun d'azun sai k'ok'arin hana y'an jarida dakeson zuwa ga Galadima sukeyi, amma suna k'ok'arin kutsowa. Tsaye Galadima yayi ya zuba dukkan hannayensa a aljihu, saida yaga shigarsu Rahma mota dasu alhaji darma sannan yanufi inda sarkin mota ya bud'e masa, y'an jaridar daketa masa tambaya ko kallo basu isheshiba ya shige mota abinsa, yayinda Muftahu ya zauna gefensa, Nuren Na a gaba. Mortar y'an sanda Na a gabansu da Bayansu, a haka akayi tafiyar. Sauran y'an sandan da aka bari suka shiga gidan domin d'akko gawar Ahmad, amma sun bincika lungu da sak'o babuma alamar an cutar da wani, sai harbi guda d'aya daya shiga jikin bango, (shima Wanda Galadima yayine sanda ya tsoratasu da cewar ya kashe Ahmad), basu samu komaiba dazai nuna Galadima d'an ta'addane, sai suka fito suna kulle gidan, amma basu tafiba harsai kotu tabada damar hakan. ............................★ Sun Isa Court d'in, inda Galadima da Nuren da Muftahu ne kawai suka Shiga, yaran dasu Alhaji Darma an kaisu wani d'akine kusada wajen. Takun takalman Galadima dake tafiya cikin tsantsar izza da nuna jinin mulki ya saka dukkan jama'ar kotun zuba masa idanu, shikam ya had'e fuska tamkar hadarin gabas Na tsakkiyar ogusta dabaya d'aga k'afar zubar ruwa, kallon kowa bayayi, gashi ya toshe idanu da Google eyeglasses d'insa da babu mai kallon kwayar idonsa. A kujerar farko irin wadda su Alhaji Mamman ke zaune shima aka nuna masa shida Nuren da Muftahu. Wani zama yayi dake tabbatarma da mak'iya shid'infa sarakine, gaba da baya kuma. Hakan ya k'ona zuciyar su Alhaji balala matuk'a, amma babu yanda zasuyi. Zaman Galadima babu jimawa saiga alk'ali ya fito, kowa ya mik'e domin girmamawa, saida ya zauna sannan duk aka zauna. Kotun tayi shiru kowa ya zubama alk'ali idanu, yagama dube-duben ta kardun gabansa sannan ya d'ago ido yana kallon jama'a, yace, “Yau shari'ar zata tafine kai tsaye batare da shigar lauyoyi Na kowanne 6angare a tsakiyaba, Dan haka muna buk'atar Wanda yay k'ara, da wad'anda ake k'ara a gaban kotu”. A hargitse su alhaji Sageer suke kallon kallo, hakama lauyansu dukya shiga rud'ani, saboda mugun shirin dayayo yau akumace ba haka za'ayiba. Shikam Galadima wani mugun murmushi yayi yana kallonsu Alhaji mansur d'in damusu wata inkiya da yatsu biyu alamar a kafta, sannan ya mik'e. Dole suma duk suka mik'e inda aka buk'aci ganinsu, dukda wajen yamusu kad'anma. Alk'ali ya kalli galadima. Yace, “kaine Wanda kai k'ara, Dan haka munason jin shin minene mafarin wannan takun sak'a kai tsaye?”. Murmushi galadima yayi, ya cire eyeglasses d'in idonsa ya saka cikin aljihu, tareda zaro handkerchief ya goge fuskarsa, yasa hannayensa biyu ya dafe katakon gabansa yana jifan waziri mahaifin Harun dawani mugun kallon daya hargitsa y'an cikinsa da tunaninsa, hakanne yasaka mutane kallon waziri suma, duk sai yaji ya muzanta. Galadima ya ta6e baki yana janye idonsa dad'an cije lips, cikin k'asaitacciyar muryarsa yace, “ya mai shari'a labarina mai tsawone kwarai da gaske, sannan cike yake da abubuwan ban mamaki da takaici masu tarin hargitsi, duk da nasan kowa yasan sunana amma zan sake maimaitawa, sunana Muhammad Sameer Saifuddin Abubakar, gidan sarauta Na fito, mahaifina shine tsohon Sarki da k'addarar ciwo ta kwantar tsawon wasu shekaru, amma lallai da sanadi, wannan kuma sanadin shine Na d'auki tsawon shekaru tundaga tasowata har zuwa yau ina nema. tun daga lokacin dana mallaki hankalin kaina nasan minene matsalar mahaifina natashi da burin d'aukar fansa, sai dai kuma tayaya? Wannan shine yayta wahalar da Muhammad Sameer a tsawon shekaru”. Galadima ya k'are maganar idonsa Na ciko da hawaye, yay murmushin takaici yana jinjina kansa da had'iye hawayen. Hakanne yasaka jikin wasu fara yin sanyi, musamman wad'anda suka k'ullaceshi da farko. Galadima ya cigaba da fad'in, “Ban taso maraya ba, amma nayi rayuwa irinta marayun, ALLAH shine gatana saikuma mahaifiyata da kakana da suka tsaya tsayin daka wajen tsayamin nazama jarumi wajen sanin wahalhalun rayuwa Na yau da kullum, duk Sana'a mai wahala kad'ance banyitaba a k'asar daba tawaba, gakuma gefe ana gwagwarmayar Neman ilimi, ga burin son sanin suwaye suka durk'usarmin da mahaifi?, ban cutar da kaina wajen nutsuwa Na fahimci rayuwa ba, hakama nabama karatuna muhimmanci saboda k'aunarsa da nakeyi, duk da banida burin yin aiki a k'ark'ashin kowa, Alhamdllh yanzu haka inada Company Na had'aka da duk shekarar duniya yake fidda wayoyin Hannu da computers dakan zagaya cikin duniya, ina alfahar da samun cikar burina sosai, Na dad'e ina bulayin Neman hanyar bincike akan abinda yafaru da Abie na, alokacin mutum d'ayane zuwa biyu ke bani gudun mawa, wato lauyan mahaifina, baffina Barrister Usman Audu, sai kakana Sarki Abdul-fatah. Ganin inata wahala sanan babu wani haske a cikin lamarin sai suka bani shawarar mizai hana a nemamin aiki k'ark'ashin wata hukumar tsaro, da farko ban aminceba, Dan irin wad'annan ayyukan basa wani birgeni, hasalima haushin masu yinsa nakeyi, Dan sun gaza binciko Wanda ya cutarmin da Abie na. A tashin farko dana nuna banaso Papi da Baffi sun k'yaleni, basu sake min magana ba, sai wata rana kwatsam wani Abu yafaru anan Nigeria, wasu y'an ta'adda sukayi mummunar 6arna a sirrin gwamnati, k'ark'ashin hukumar DSS. wannan 6arna ta rikita Nigeria sosai a lokacin, shekaru 10 kenan inhar ban mantaba, a lokacin nagama bautar k'asata anan Nigeria ina shirin komawa india, bansan ya akayi sukasan nasan Computer ba, har masarauta akazo aka rok'i mai martaba akan Na taimakesu. Da farko kam naso bijirewa amma babu abinda iyayena zasuce nayishi banyiba inhar bai sa6a shari'a ba, nasanma bazasu sakani wannanba, bisa umarnin mai martaba Na amince da gwadawa idan zan iya, haka akaje dani headquarters d'insu, tun hawan Computers d'in danai a tashin farko Na gane da had'in kan waaunsu aka kwashi bayanan, sannan masu kula da Computers d'in sunada buk'atar k'arin ilimi ma gaba d'aya. Cikin sauk'i Na d'akko bayanan da aka d'auka Na dawo musu dashi, sannan nasaka musu securitys masu tsaurin gaske daba wani mahaluki dazai kuma musu irin wannan kutsen. Ni ban d'auki abinda nayi matsayin komaiba, amma agaresu sun girmamashi, sunkuma biyoni har gida da rok'on kasancewa a cikinsu amma nak'i Sam, nama tattara Na koma India, Ashe sunata bibiyata ta wajen kakana, to shima dama yana burin nayi aikin, Dan haka yabasu goyon baya, sannan yaje har India ya sameni da batun, ya nunamin ta wannan hanyarne kawai zan iya binciko abinda ya faru da mahaifina cikin sauk'i, hakama Baffi ya fad'amin a lokacin, Na zauna nayi nazari dakuma samun kwarin gwiwa daga Mahaifiyata. Rana d'aya sai nima naji yakamata Na amince, Dan haka Na amince, tundaga lokacin nashiga cikin hukumar CID nima, saidai ina musu aikine cikin sirri, a hukumarma ba kowa yasan daniba, tunda ni komai ta computer nake gudanar dashi. Sir Isa Maharazu shine ya taimaka min wajen binciko file Na binciken case d'in mahaifina, Wanda tun kusan shekaru 8 mai kula da case d'in ya rasu, Wanda kuma suke ta fannin y'an sanda suma sukayi shiru, daganan aka ajiye case d'in gefe kawai. Tun a file d'in nafara cin karo da sunayen wasu daga cikinsu Alhaji Lawan tanderu. Nasha mamaki kwarai da gaske amma sai banyi wani yunk'uriba, ina wata shida da aiki wani yaso min kutse a cikin Computer, ta silarsa nagano uban gidansa, har zuwa Kansu Marigayi Alhaji Labaran kachia. Tundagafa wannan lokacin saina tsananta bincike da kwakwalwa dakuma tannin aiki, bisa taimakon sir Isa, mun baza yara cikinsu Tanderu batare da sunsaniba, kullum kuma cikin bin diddigin motsinsu suke. Kwatsam sai Tanderu ya rasu sanadin had'in mota, babu jimawa shima Alhaji Labaran khacia ALLAH yamasa rasuwa sanadin rashin lafiya. daga nan saina d'an dakatama gaba d'aya da wani bincike Na koma gefa Na zuba musu ido kawai. Saida Na d'auki kusan shekaru biyu ban sake wani yunk'uriba sai kwatsam muka wayi gari mijin Yayata Haneefa yayi had'arin Mota, saidai kuma a ranar ne aka turomin massage daya nuna accident d'in nashi akwai saka hannu a ciki, dayake bai rasuba a lokacin sai a asibiti bayan awanni uku da kaisa, Alhaji shehu Darma abokinsa ne Na kut da k'ut sannan d'an uwansa, Dan haka yana tare damu a wajen, saina matsanta akan tambayarsa kozai fad'amin akan miya faru dashi kafin had'arin? Bai iya cemin komaiba sai murmushin k'arfin hali da yayi yana kallon Alhaji shehu har numfashinsa ya k'are, wannan kallo ya tsayamin a rai sosai, Dan nagaza mantawa dashi, abinda Yakuma k'arfafa min zargin Alhaji shehu shine Aunty Mimi Na fita daga takaba sai Yace yanason aurenta, nine Na hana, nama tattarata gaba d'aya itada y'ay'anta Na maidasu india, dukda dangin mahaifin yaran sunso d'aukarsu suma. Dama can lokaci-lokaci Alhaji shehu yakanbi mijin Aunty Mimi suje duba Abie, dan haka ko bayan rasuwarsa bai daina zuwaba, abinda na fara fahimta shine Samha d'iyar marigayi tana tsoron Alhaji shehu, amma shi yana tsananin nuna mata kulawa dayin kaffa-kaffa da ita a gaban mutane. Wannan ma yasa na kuma saka ido a kansa, abinda Na fara karo dashi shine Alhaji shehu yana tursasa Samha ta hanyar mata barazana akan ta d'akko masa wasu sirrikana”. Galadima ya murmusa cikin takaici yana gyara tsayuwa da goge fuskarsa da handkerchief. Yaciga da fad'in, “Tunda Na fahimci hakan saina jata a jikina, nakuma dinga ajiye mata dukkan abinda yasaka ta d'akko, itako data gani saita tura masa saboda tsoron barazanar da yake mata. Suma sauran Na cigaba da bibiyarsu suda ayyukansu, so banida matsala da sauran mugayen halayyarsu, nidai kawai wadda ta had'amu nakeson Sani, Dan Na gano sun gana da mahaifina ana gobe abinda ya sameshi zai sameshi, kuma yafito daga d'akin tattaunawar ransa a 6ace. Batanci da akaimin a shekara d'aya data wuce cikin jaridar manuniya shine mafarin yalwatur haske a matsalolina, dukda Na fahimci ankai tsawon shekaru ana bibiyar dukkan al'amurana, kuma inhar Nazo k'asarnan kullum cikin bibiyata ake, domin rufe bakin mak'iyana Na auri wadda sukaso sakawa a matsalar dabatajiba bata ganiba, wadda a yanzu Alhmdllh itace uwar y'ay'ana, nasan hakan ya girgizasu a lokacin kwarai da gaske, adalilin zama da ita nama fahimci abinda ban fahimtaba da farko, Dan da Duk zargina ko da itane aka had'a kai wajen Neman 6atamin suna, amma sainaga dukba haka baneba, ya mai shari'a Alhaji Auwal Fharuk sai shine surikina mahaifin matata, kuma anyi yink'urin kasheshi watanni kusan 7 da suka shige, saidai ALLAH ya k'addara yanada sauran kwanaki a gaba, bisa dalilin yun k'urin kisansa ne kuma Na fara karo da alak'ar case d'in mahaifina dashi, hakan kuma tafaru bisa sanadin matata, data dinga zak'ulomin wasu masu alak'a da mahaifinta kuma Na jikinsu tanderu, irinsu Mamman k'afur, Alhaji Halluru, saikuma daga baya ga SD, wato Alhaji shehu Darma, Wanda shine aka saka yake bibiyar Alhaji Auwal Fharuk yana masa barazana, satar yarana da akayi a ranar sunansu ta kawo bayyanar aminina d'an uwana cikin case d'in mahaifina daban ta6a tunanin kasantuwarsa a cikiba, wato Harun d'an gidan waziri, shine wazirin mahaifina shine kuma wazirin Sarki Na yanzu, ina cikin rud'anin Hakan saikuma ga Alhaji Rabilu ya bayyana a gareni shida Badi d'a ga mai dokuna a masarautarmu, Wanda tun ina k'arami Na sanshi, amma daga baya ya 6ata 6at. Bayanan wad'annan bayin ALLAH da bincikena Na had'a suka tabbatar min da zargina akan wad'annan mutanen, nasan abune mai wahalar gaske samunsu cikin sauk'i da fahimtata da duniya zatayi akan zargin danake musu, shiyyasa naza6i yin Garkuwa da yaransu bisa tursasasu tilas sufad'i abinda ke ransu da Wanda suka aikata. Dukkan Wanda ya shigo cikin labarin nan nawa akwaishi a wajennan, mijin yayatane kawai bayada rai sai mahaifan Badi, dakuma wasu daga cikinsu da sukabar duniya, Dan haka ina rok'on wannan kotu data nemo dukkan Wanda Na ambata domin jin ta bakinsa”. Alk'ali ai yama kasa magana, sai kad'a kai kawai yake mamaki da al'ajabi Na cinsa, yayinda kotu tayi tsit kowa yana k'ullawa da kwancewa da tausayin Galadima, irinsu Alhaji Halluru kam ai cikine ya d'uri ruwa, sunsan dai tasu tagama k'arewa kam, Dan yau ranar bankad'a Ce da walle-walle. Alk'ali yad'anyi rubuce-rubucensa sannan ya buk'aci ganin Badi da Alhaji Rabilu, Galadima kuma yaje ya zauna. Alhaji Rabilu da Badi sun bayyana a gaban kotu, hakan ya kuma hargitsa hanjin cikin Waziri, yana mamakin dama Badi bai mutuba? Amma su hak'ilu sukazo sukace ya mutu a wancan lokacin, dan agabansu mai besfa ya kad'eshi, innalillahi ya shiga ambata a zuciyarsa, sai zufa ke jik'eshi, sauk'insa ma akwai malun-malun da rawani a jikinsa, Abba Hayatudden kallonsa kawai yake da tsantsar tsana da mamakinsa. Duk yanda Badi da Alhaji Rabilu sukaima Galadima bayani haka suka maimaita a gaban kotu, wasu harda hawayen tausayinsu suke matsewa, Alk'ali yace, a kawo Alhaji Auwal Fharuk Dan Badi yaga idan shine yabama camera. An kawo Abba, Wanda Alhmdllh jikinsa yayi sauk'i sosai, saidai abinda ba'a rasaba Na k'arfi, kallo d'aya Badi yayma Abba ya ganeshi Dan bai canja masaba sai canjin girma irinnan shekaru, hakama Abba ya gane Badi sarai Dan shima d'in bai canja masanba, aiko suka rungume juna kowa yana hawaye, Abba yana fad'in “Bawan ALLAH Dama baka mutuba a waccan ranar?”. Shima Badi cikin kuka yace, “ban mutuba, sai daga baya ne Na farfad'o a wajen”. Alk'ali ya ankarar dasu cewa a kotu suke, kotu kuma Na buk'ar jin bayani daga bakin Abba, ta Yaya Camera ta dawo hannunsa?. Abba ya dai-daita tsayuwarsa sannan ya gabatar da kansa ga kotu, ya d'ora da fad'in “shekaru 22 kenan da suka shud'e wannan camera take a hannuna ranka ya dad'e, nakuma sametane ta hanyar kad'e wannan bawan ALLAH danayi da abin hawana a wancan lokacin, saboda ya shigo hanya yana matsanancin gudun dabansan mafariba sai yanzu danaji a ya fad'a a gaban kotu. bayan na bigeshi numfashinsa Na Nuna alamar bankwana da gangar jikinsa ya d'auki wannan camera yabani acikin akwati da sunan amana, yakuma ambatamin sunan wad'anda zanba kamar yanda yafad'a, daganan numfashinsa ya tsaya cak da aiki, ina cikin k'ok'arin taimakonsa saiga wasu mutane da gudu da makamai sun dosoni, tsoro naji, Dan inada tabbacin shima sune suka biyoshi, saboda son isar da amanar daya bani inaji ina gani badan nasoba Na tsallakesa Na gudu, Dan nasandai zasu iya kwatar abinda yabani d'in. tunda camera d'in nan ta dawo hannuna ban sake barci mai dad'iba, kullum burina da tunanina tayaya zan Isar da amanarta Na huta, tsawon shekaru ban ta6a fuskantar wani k'alubale akanta ba, Dan ko iyalina babu Wanda yasan da zamanta a hannuna, matata tasha tambayata idan taganni cikin damuwa amma banta6a fad'a mataba, kwatsam cikin laluben Wanda zan bamawa sai Marigayi Alhaji Abdul-hakeem Uba tsohon Governor d'inmu ya fad'omin, Dan ganin yana auren d'iyar tsohon Sarki wadda tana d'aya daga cikin wad'anda akace nabamawa, to lallai anan Alhaji shehu SD yasan Camera Na hannuna, Dan tabbas yaji zancen da mukayi da Alhaji Abdul-hakeem d'in ta hanyar la6ewa, aranar da mukayi zan bama Alhaji Abdul-hakeem camera ya damk'ata ga matarsa sai aka samu akasi wani aiki ya tasomin Na manta ban fito da camera ba, amma mun had'u da shi marigayi Alhaji Abdul-hakeem Na bashi hak'uri da sanar masa uzirina, shikuma SD a tunaninsu nabama Alhaji Abdul-Hakeem wannan camera, shine suka hari rayuwarsa da nufin kar6a kafin ya kaima matarsa, inaga daga baya da suka fahimci babu Camera d'in a hannunsa shine suka juyo kaina. Sunta matsama rayuwata da barazana iri-iri, kiran waya da sauransu, duk number da suka kirani da ita gobe bada ita zasu kirani ba, hakkane ya sakani ware sim card guda kawai dansu, babu Wanda ya sanni dashi, sai matata Dana saka number cikin wayarta batare da itama tasan hakanba, nayi hakanne saboda watarana koda ALLAH yabasu nasarar kasheni d'in. A lokacin da akaima yarana 6atanci da Galadima lallai hankalina ya tashi matuk'a, amma daga baya danayi nazari saina gano maybe su SD ne suka aikata hakan domin 6atamin suna, hukuncin ALLAH kuma saigashi mai martaba Sarki jalaludden da mai martaba Sarki Abdul-fatah sunzo nemawa d'ansu Galadima auren yarinyata da abin yafaru akanta, dukda a 6adda kama sukazomin ni sarai Na ganesu, amma ko y'an uwana ban sanarmawaba, abinda yabani k'arfin gwiwar aurar musu da yarinyata shine Isar da amanar hannuna cikin sauk'i, saikuma aminin mahaifina Baba mai kanwa yace nabasu, Dan shine kawai yasan da zaman Camera a hannuna, shima bani Na sanar masaba, bankuma San a ina yajiba. A randa za'akai y'ata gidan mijinta a ranar Na saka wannan camera da takarda cikin wani kwali Na sakashi a kayanta batare da tasaniba, bansaniba kota gani? Dan cikin gifts d'inta data samu a hannun abokan mijinta ranar dinner d'in auranta Na sakashi, nabama d'an uwantane Abdul-Hameed babban d'ana yabata batare da shima ya san minene a ciki ba. Hikimata anan idan tagani tabama mijinta batare da kace Na ceba. SD bashikad'ai ke bibiyar rayuwata ba, Dan akwai masu sakashi yazomin da farashin kud'i masu tsoka akan camera d'in amma nayi kunnen uwar shegu dasu, hakanne yasakasu k'ok'arin salwantar da rayuwata wai tunda Na hanasu camera, nasan sunajin tsorone saboda Na kusantu da Galadima a lokacin, zan kuma iya bashi camera d'in, saidai abinda basu ma saniba tuni Camera d'in tabar hannuna. Alhaji Halluru abokinane Dan school mate d'inane, ada babu wata alak'a mai k'arfin tsakanina dashi, amma daga baya sai yayta Jana a jikinsa, ban fahimci manufarsaba dagashi har Alhaji Mamman, Dan da zuciya d'aya ni nake zaune dasu. Sai wannan karon da suka tabbatarmin da zulwa jahainin fuskarsu, sannan suka tursasa y'ay'ana biyu Dana d'auka nabama y'ay'ana Alhaji Halluru aure saboda yarda wai su d'akko musu camera a d'akina kosu kashesu dani dakuma iyayensu mata, sun razanasu da cewar sun dasa bomb a gidana, agabana duk suka sanar musu a waya. Abinda yasa ban damuba nasan k'arya suke, sannan Camera d'inma bata gidan, duk k'ok'arin lalatama Galadima sirrika da sukayi agabana sukayishi, amma ALLAH baibasu nasaraba, jin asirinsu zai Toni ta hanyar Garkuwa da y'ay'ansu da Galadima yayi shine suka shak'amin abinda ban saniba, daganan ban kuma Sanin ina kaina yakeba sai a asibiti yamai shari'a”. Wannan bayanima Na Abba ya girgiza zukata sosai. Dan har alk'ali kasa motsawa yayi, saidai yaja kusan mintuna biyu sannan ya sauke ajiyar zuciya mai k'arfi. Ya buk'aci a kawo masa camera nanda awa 2 kacal. Anbar lokacin a matsayin hutun kotu. Babu Wanda yaso matsawa konan da can, kowa burinsa dai camera ta iso aga mita k'unsa. Galadima ya kira Munaya, yace ta shirya ga Sarkin motanan zasuzo da Nuren su kaita masarauta ta duba cikin gifts d'inta Na Aure data samu Abba yace camera Na ciki. Dayake a labarai an nuna takuma gani, sai kuka dama takeyi da mamakin miyasama bata duba gifts d'in auren nataba tun wancan lokacin? Koda yake bata dad'eba a Nigeria suka wuce India, itakam a dukkan zaman da suka d'an tayi idan sun dawo bata sake bi takan gifts d'inba, to kawai tace masa ya yanke wayar, Dan yanzu babban burinsa kawai a tabbatar camera d'in tana wajen nata. Tana gama shiryawa sarkin mota yazo da Nuren dakuma police, bata d'auka yaro ko d'ayaba tafito suka tafi masarauta. Sun iske masarautar tsit, tamkar anyi sharar mutane, kowa Na sashensa abinda ke faruwa yama zukatansu murus, hannu kawai take iya d'agama hadiman sashen nasu dake gaisheta, basu damuba, dansunsan tana cikin wani yanayine. Sashen nasu yayi y'ar k'ura, saboda kwana uku babu kowa a ciki, Munaya kanta tsaye bedroom d'inta ta shige kawai, ta bud'e wardrobe nata tashiga fiddo gifts d'in aurenta data tara gefe, tareda Na haihuwar su Abdurraheem. d'ai-d'ai taita farkesu, idan taga bashi bane ko bud'awa batayi take jefawa saman gado, tasha wahala matuk'a kafin ta gano akwatin da idonta ya ta6a tozali dashi a d'akin Abba itada Munubiya, rungume akwatin tayi ta fashe da kuka maiban tausayi, ana haka kiran Galadima ya shigo wayarta, share hawayenta tayi ta d'aga. A d'arare yace, “kin hanshi?”. Cikin dariya da kuka ta amsa masa da eh ta gansa, shima murmusawa yayi, yace, “maza Ku tahoto, mintuna 46 suka rage a lokacin da alk'ali ya bada, sonake kawai a kammala shari'arnan a yau”. Munaya ta amsa da “to gamunan.................✍🏻 *_“insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu, koma mike cikin camera d'in dai zamu gani, nima Na k'osa nagani a wuce wajen😬🤦🏻‍♀”_*. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [8/4, 3:27 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻1⃣9⃣ .................Su Munaya sunyo nisa da tafiya danja ta tsaidasu, kamar daga sama suka fara jin harbi, y'an tsirarun mutane dake bisa titin suka fara guduwa, dan titin wajen baicika yawan mutaneba, kasancewar wajen tamkar sabuwar anguwane kuma gefen gari kad'an, itace hanya mai sauk'i da zata iya kaisu da wuri shiyyasa suka biyo..... Batakai k'arshen tunanintaba taji wani azababben zafi a damtsen hannunta, ko kad'an bataji k'arar wannan harbinba (dam inhar harbi zai shiga jikin mutum aishi bazaiji k'arar bindiga ba) kallon inda akayo Harbin Munaya tayi, glass d'in ya huda ga wani garjejen k'ato yayo wajen motar, a kid'ime ta kalli sarkin mota da hankalinsa shima yake a tashe, sai zufa yake yana waige-waigen ganin yanda police d'in suka fita sunason basu kariya. Cikin k'arfin hali Munaya race, “Sarkin mota, ka kar6i Camera d'in nan ka hanzarta kaita kotu, ya tabbatar min lokacin buk'atarta tayi, karka sanar masa komai harsai shari'arnan ta kammala dan ALALH, inason burinsa yacika koda ace zan rasa raina a yau, please karka damu sarkin mota jeka, maza jeka kar Mara imaninnan ya k'ara so. Badan sarkin mota yasoba ya kar6a ya fice da sauri cikin dabara, saboda Munaya tabashi tausayi, ga harbi ta samu, amma bata kanta takeba ta cikar burin mijinta takeyi. Fitar sarkin mota tayo dai-dai da isowar garjejen k'atonan, ya bud'e murfin motar yana fisgo Munaya waje, fad'owa tayi kanta ya bugu da kwalta sai jini kawai, tuni numfashinta yafara fita da k'yar, dishi-dishi take hango wani Na dukan Nuren da bakin bindiga yana k'ok'arin kare kansa da kiran sunanta yana mik'o hannu, amma ina, sun riga sunci k'arfinsa, idanunta suka lumshe a hankali, yayinda wasu hawaye masu zafi suka gangara ta gefen kumatun data fad'in, fuskarta d'auke da murmushin k'arfin hali. Nuren daketa kwala mata kira a rikice yana mik'o hannu, dukda dukansa da ake, ya zube a k'asa yana fashewa da kuka maiban tausayi da ambatar “please Munaya karki tafi kibarmin d'an uwa, ke wani yankin farin cikinsace mai matuk'ar girma ple...... Shima baikai k'arshenba ya sulale k'asa saboda dukansa da sukayi a kai. Wani dake bincika camera d'in a motar ya juyo a fusace yana fad'in “babu camera d'in fa boss”. A rud'e Boss d'in dake tsaye gaban Munaya ya taka hannunta da mugun takalminsa yayo wajen, ko motsi kuwa batayiba alamar ruhinta yabar gangar jikinta. Ture yaron nasa yayi yafara lalube da kansa, hankalinsa yakai gaban motar. yace, “Ina driver!!? ”. Yanda yay maganar a rikice ya saka yaran rikicewa suka hau waige-waige, sarkin mota dayay nisa a gudu yana jiyo ihun ogan, saiya k'ara k'aimi. Wani yace, “gashi can zai gudu da camera d'in ”. Tuni suka rufoma sarkin mota baya a guje, shima yacigaba da gudu iya k'arfinsa. Cikin amincin ALLAH saiga wani mai mashin tamkar an jehoshi, ya tsaya yana fad'in “maza hau muje”. Sarkin mota ya haye, mashind'in nabarin wajen suna k'arasowa, Dutsuna suka d'auka suka dinga jifansu sarkin mota suna binsu da gudu, amma ALLAH bai basu nasaraba. Hardai ubangijin sammai ya kaisu court lafiya. Sai lokacin Na lura Ashe Ahmad ne yaron Alhaji Bana, ya kalli sarkin mota yana fad'in “Maza kakai, yanzu haka ita kawai ake jira, kasa nutsuwa a ranka kar boss ya fahimta balle yakasa nutsuwa a shari'ar shima, yanzu haka suma police zasuje su taimakesu, muma can zamu tafi da sauran y'an uwana”. Kai sarkin mota ya jinjina, ya k'arasa gaban k'ofar kotu yay knocking yana share hawaye da tausayin Galadima. Anzo an bud'e masa aka shiga dashi, dama camera d'in kawai ake jira. A can kuwa suma saiga Police an k'aro, wad'anda suke tare dasu Munaya su 6 ne kawai dama, gashi bawani isassun kayan aikine dasuba, bindugun hannunsu babu mai bullet, sun daki d'aya yasuma, d'aya kuma yasamu ya sulale domin kira yasanarma ogansu abinda ke faruwa, yayinda biyu suka gudu, biyune kawai a wajen, sukuma sunyi musu yawa y'an ta'addan. Isowar police d'in ta saka wasu a cikinsu yunk'urin guduwa, saidai ina, ALLAH yakan ara maka rana, randa kuma zai kamaka babu hanyar ku6ta, dukansu ram akayi dasu, dukda wasu sunso yin gardama, duk aka zubasu a mota, yayinda Ahmad yasake dawowa shi da Yassar tareda Ambulance, suma su Munaya da Nuren aka kwashesu😭. ...............................★ Tunda Galadima yaga sarkin mota ya kawo camera hankalinsa bai kwantaba, dakuma yaso had'a ido da Sarkin mota shi saiya kauda nashi, yak'i yarda su had'a idon....... Maganar Alk'ali ta katsema Galadima tunaninsa, yayinda yake bada Umarnin a bud'e camera d'in, takardune aciki guda uku, d'aya abbane ya rubutata yanama Galadima bayanin yanda akai camera tazo hannunsa, d'aya kuma sunayen dukkan wad'anda ke bibiyar sa akan camera d'in ne, d'aya kuma wadda mutumin farko d'an uwan baba Rabilu daya bada camera d'in ne ya rubuta ce. Ita kad'ai alk'ali yabada umarnin karantawa, yayinda masana keta k'ok'arin saita camera da TV dake kotu suma, Wanda Galadima ne ke k'ara sanar musu dukkan dabarun daya kamata suyi daga inda yake tsaye. Abinda takarda ta k'unsa shine..... *_Assalamu alaikum_* _Sunana Habu, wannan takarda ina fatan ta iso agareku, ko yarima, ko gimbiya ko matar Sarki mahaifiyar su yarima, Ku duba wannan camera d'in, duk yanda aka k'ulla faruwar ciwon mai martaba da wad'anda suka kulla suna a ciki, nidai nasan tawa ta k'are, dan tunda suka ganni ina d'oukar sirrinsu saisun kasheni, wata uku kenan ina 6oye-6oye, yaudai Na yanke shawarar fito fili Na baku koda hakan yana nufin zan mutu, dama can kwanana sun k'arene, koma basu nayi saisun kasheni, ballema bazan ta6a basu d'inba, ALLAH yabama mai martaba lafiya da tsawon kwana mai amfani, yakuma baku ikon hukunta wad'annan tsinannun masu jinin Fir'auna a jiki, wad'anda mulkine da tara duniya kawai a gabansu ba al'ummar k'asarsuba, duk yanda zakuyi karkubar la'anannnun nan yin mulkin al'umma, subasu cancanci zama shuwagabanniba._ *_Bisalam_*. Kotufa tayi tsitt, ko tarin wani bakaji sai k'arar fanka, yayinda zufa tagama jik'e su Alhaji balala sharkaf, kallo d'aya zakai musu ka fahimci ruwafa ya k'arema d'an kada. Alk'ali baice komaiba, jira kawai yake camera ta daidaita ajikin TV kowa yagani, matsalar camera Ce irin ta da, shiyyasa take bada wahala, da k'yar dai cikin amincin ALLAH ta kawo, tofa, saidai kalar da take nunawa White and black, ga wani rawa-rawa da takeyi saboda ba nutse aka d'aukaba, kuma da alama ana yayyafine. Dagani wajen wani ke6antaccen wajene daba kowa ya isa shigaba, shikansa d'an jarida habu kota Yaya yayi hakan? ALLAH kad'ai ya Sani saishi, gashi bashida rai balle mu Sani. Mutanene da ak'alla sunkai 20 a wajen. Alhaji balala, Alhaji Mansur, Alhaji Lawan tanferu, Alhaji Bana, Alhaji Abdul-Naseer, Alhaji Labaran khacia, Timothy, Hajia A'i, Victoria, Miracle, Alhaji Sageer, William, Josaya bamma, Kabiru Ibarheem, Alhaji Mamman, Waziri, Sai wani Sarki daba wani k'arfin ikone dashiba, yama rasu tuni, tun ciwon Abie babu dad'ewa, sai Mahaifin Gimbiya Zulfah uwargidan Sarki, shima sarkine mai fad'a aji, Sai mahaifin Mama Fulani😱, sauran Biyun turawane. Duk suna zaune kowanne da kwalbar coca-cola a gabansa (sannan shinsa sai manya🤣). Alhaji Lawan tanderune ya mik'e yafara jawabi kamar haka. _Masu girma saraki dake wannan waje, da bak'inmu (turawa) sai abokaina shak'ik'ai ina muku sallama gaba d'aya_ Duk suka amsa a tare. yaci gaba da fad'in, _Muduka nan mun tarune akan mak'iyinmu guda d'aya, Wanda ya tare mana gabas ya tare mana yamma, hakama kudu da arewa, mun bishi ta lallami akan yabamu goyon bayan cikar burinmu amma yak'i, yana wulak'antamu saboda yaga ALLAH yabashi k'arfin iko da izzar mulki a hannu, a daren jiya mun yanke shawarar kasheshine kowa ya huta, amma yanzu mun fasa hakan, zamuyi masa abinda saiya gwammaci yazama gawa, dan zai rayune shiba mutumba Shiba butun butumiba, ahaka naman jikinsa zai ringa ru6ewa sashe-sashe, mukuma zuwa sannan mulkinnan dai dayake ganin bazai dafa mana muyiba ya dawo hannunmu, dan mungaji da mulkin soja hakannan, gashin kanmu muke buk'atar ci koya kukace?”_ Hannu suka d'aga suna fad'in eh hakane hakane. Alhaji Lawan tanderu yayi dariya yana gyara babbar rigarsa, ya d'akko wani ruwa a kwalba yana nuna musu, _“kunga wannan itace gubar ruwan allurar da za'ai masa, ita cikin mintuna biyu zuwa biyar take fara tasiri koba haka kaceba Mike?”._ Cikin turawa biyu dake tare dasu d'aya ya gyad'a kai yana murmushin mugunta. Gaba d'aya suka sanya tafi, raf! Raf! Raf!, saikuma suka koma tafawa da musabaha a junansu (irin sun samu cikar burinsu d'innan). Tanderu yacigaba da magana bakinsa a washe. _“Wannan aiki ba kowane zai mana shiba sai wazirinsa, Munaso da asubahin yau kamasa wannan allura dakagani, inamai tabbatar maka inhar ya Idar da sallar to bazai shiga gida da kansaba”_. Waziri mahaifin Harun ya kar6a yana washe baki tamkar gonar auduga, da fad'in “lallai nafi kowa farin ciki da samun wannan dama, domin kobabu komai zanyi maganin mak'iyina da kaina, daga yanzu sainaga da bakin dazai kuma cin zarafina da jifana da kalaman banida hali, toshi mai halin saiya cigaba da shukashi muda bamu dashi muyita girba munakaiwa gidanmu munaci....”. Gaba d'aya suka kwashe da dariya suna tafawa, a Na wannan dariyane Alhaji Bana idonsa yakai ga camera, alamun yaga habu kenan, ajiye k'aramin kofin silver dake hannunsa ya zuba coc yayi yana mik'ewa zumbur. Sauran suka fara tambayarsa mike faruwa?, tuni habu daya farga dasu ya shek'a da gudu. Daga nan ba'a sake nuno kowaba, sai gudu da habu yakeyi da hakkinsa, Camera d'in Na wani shuw-shuw harma aka bar ganin komai. Kwakwkwaran Motsi kowa ya kasayi acikin Court d'in, Galadima ya duk'ar dakai yana kallon k'asa hawaye Na zirara suna d'iga, hakama Abba Hayatuddin kuka yake saboda tausayin d'an uwansa da takaicin waziri daya kasa zama kusa dashi yanzun, ga takaicin wai harda kakansu Wanda ya haifi mahaifiyarsu, shin shikuma miye matsalarsa da d'an uwansa ne? Kenanma mama Fulani mahaifiyarsu itama tasan komai? Innalillahi wa inna'ilaihiraji'un, wannan wace iriyar masifacene hakan?. Alk'ali daya buga gudumarsa a sanyaye ya katse tunanin mutane da yawa dake cikin kotun, cikin sauke nannauyan numfashi yace, “yanzu babu tanderu a duniya, shin ko akwai mai wakiltar wannan group a yanzu?”. Su Alhaji balala da duk jikinsu yay lak'war kunya da nadama duk sun lullu6esu sukayi tsitt. A fusace cikin daka tsawa Alk'ali yace, “waishin! Ba'a jini bane?!!”. Jiki Na rawa Josaya bamma ya mik'e, tsufa sosai ya kamashi, danma akwai jin dad'i tattare dashi, ko a wancan lokacin dagani ya girmi tanderun ma gaba d'aya. Wani cikin ma'aikatan kotun yaje inda alk'ali yake suna magana k'us-k'us, komi yake fad'a masa oho, nagadai alk'ali yayi alamar a kawosu, wancan ya sakko, shikuma alk'ali ya maida hankalinsa ga Josaya bamma dake k'ok'arin shiga inda ake buk'atar ganinsa. Josaya Yaje inda ake tsayawa ya tsaya, Alk'ali ya kallesa cike da tsantsar tsana yace, “kotu tanason jin shin minene kuka nema ga adalin Sarki mai gaskiya da son ayi gaskiya irin Sarki Saifudden yak'i baku goyon baya har kuka nakasashi?”. Josaya bamma ya gyara tsayuwa kansa a duk'e saboda kunya. Yace, “Ya mai Shari'a, mu mun kasance y'an k'ungiya d'aya masu burin kafa gwamnatin farar hula a wacan lokacin, mafi yawa acikinmu tare mukayi karatu a landan, tunkuma munacan wannan shine babban burinmu, dan haka koda muka dawo najeriya muna kan wannan buri, duk da mulkin soja shike gudana a k'asar tamu, kuma babu wani mahaluki daya Isa yin koda kwakwkwaran tarine, da farko mun fara janyo wasu mutane da yawa suka shigo jikinmu, sannan muka farabin sarakunan gargajiya Na kudanci da arewaci dan samun had'inkai, wasu sun amince mana, wasu kuma sun nuna babu ruwansu, Sarki Saifudden yana sahun farko Na manya-manyan sarakunan gargajiya da akeji dasu da girmama maganarsu a arewaci, munada yak'inin inhar ya bamu goyon baya mun gama samun abinda mukeso, wannan yasa muka fara binsa ta k'ark'ashin k'asa, wato su Mike sukaje ga wazirinsa suka gana da samun manya-manyan sirrika a wajensa, sunje da kwanaki biyu muma sai muka tunkari Sarki Saifudden bisa jagirancin Waziri. Cikin lalama da rok'o muka fahimtar dashi manufarmu, amma saiya fusata, yakuma jamana gargad'i karya kuma ganin koda masu kama damune a masarautarsa, kuma lallai shi da kansa zai nemi shugaban k'asa mai mulkin wancan karon ya sanar masa manufarmu, munta k'ok'arin fahimtar dashi amma yak'i saurarenmu, daga k'arshema saiya koremu daga masarautarsa, wannan shine dalilinmu Na shirya cewar zamu kasheshi, amma daga baya saisu Mike suka kawo mana shawarar masa allurar poison, bamusan ya akayi wannan d'an jarida ya San da shirinmuba harya biyomu inda muka ke6e dan tattaunawa, munta bibiyar rayuwar d'an jarida amma bamu sameshiba, marigayi tanderu ya k'arfafa mana gwiwa akan karmu fasa yin shirinmu, waziri zai kula da motsin kowa a masarautar, a ranar Waziri yatafi da wannan allurar guba, dakuma asubahin washe gari yacika mana aiki, bamu sakejin labarin d'an jarida ba saida Sarki Saifudden yacika watanni uku da fara jiyyasa, saigashi cikin yaranmu wani ya samoshi, sun bishi dansu kasheshi amma saiya 6oyema ganinsu, Ashe yabi motar mai dawakai ne daya gani akasuwa yazo sayen abincin dawakai. Wani bawane yaga wannan d'an jarida tareda mai dawakai a barga, shikuma bawan yana d'aya daga cikin wad'anda waziri ya baza a masarautar domin saka ido, dan yasan komai Daren dad'ewa d'an jaridarnan saiya so kawo camera d'in a masarautar, a lokacin yasaka ancigaba da bin d'an jarida, yakuma k'yale su mai dawakai har zuwa dare yaje garesu. Camera dai tacigaba da walagigi, har muka samun kashe d'an jarida, a lokacin bamusan Alhaji Rabilu munafuki bane yasan komai, har yazo ya shiga jikin mu da cewar yazo shiga tafiyarmune, Ashe munafuki yasan komai, dan bamuga fuskarsa ba lokacin damukaje fadamar bayan gari, shi Badi shikad'ai muka gane tunda dama waziri ya sanar mana. Muncigaba da Neman Badi har tsawon shekaru 4 amma ko labarinsa babu, saidaga baya cikin shekara ta biyarne muka samu labarinsa a wani k'auye, munta bibiyar rayuwarsa daki-daki, har randa yabaro k'auyen muka cigaba da binsa, lokacin daya farga damu shine ya gudu Alhaji Auwal Fharuk ya bigeshi da besfa, lokacin da yaranmu sukazo shi Alhaji Auwal Fharuk saiya gudu, dan haka basuga fuskarsa ba, shikuma Badi ya suma, a tunaninsu ya mutu, suka daddike gawarsa suka dawo suka sanar mana babu camera d'in a hannunsa, sannan kuma ya mutu, amma suna k'yautata zaton yabama wani kafin zuwansu, kilama mai besfa d'in daya bigeshine, bamu hak'uraba, mun cigaba da lalube dukda bamusan wanene ba, ana cikin hakane kuma muka samu damar kar6ar mulki, burinmu ya cika, Alhaji Labaran Khacia yazama shugaban k'asa kamar yanda muka tsara, dan dukya fimu arzik'i a lokacin, saidai kuma yana shekara biyu kacal da hawa mulki Alhaji Lawan tanderu ya rasu sakamakon had'in mota, shugabanci k'ungiya yadawo hannuna, Tanderu bai dad'e da rasuwa ba shima Alhaji Labaran yakwanta jiyya, kwanansa baifi 6 ba ya mutu shima, lallai wad'annan rashin sun girgizamu matuk'a, har yanzu kuma mun kasa mantawa. Tun daga wancan lokacin duk Wanda zaiyi shugabanci a k'asarnan da taimakonmu yake yinsa, kuskuren da mukayi shine mantawa da Sarki Saifudden nada d'a namiji, kuma komai Nisan lokacin zai iya Girman da zaibi ba'asin ciwon mahaifinsa, gaba d'aya sai hankalinmu ya k'arkata ga son samun Camera kawai, a tunaninmu damun sameta dukkan magana ta k'are. Har lokacin da muka fahimci Alhaji Rabilu shima munafukinmu ne, shine muka titsiyeshi akan camera, amma yace bai saniba, Alhaji Shehu ya d'auki mataki a kansa, dan dukkan Wanda yasan da zancen camera burinmu mu kaudashi kawai magana ta k'are, Bamu farga da yarima Sameer ba sai lokacin da ya fara bibiyarmu, Ashe a time d'in shi C.I.D nema, mukuma duk bamu saniba, da taimakon d'an waziri Harun muka samu bayanan sirrin Documents d'in shi yarima Sameer, dan haka Kabiru Ibraheem da shima masanin Computer ne ya shiga yimasa kutse, dan munason musan shin yarima Sameer yana sane da mune? Inhar yana sane damu mukaudashi shima. Saidai kuma yaron ya wuce da dukkan tunaninmu, yanda muke bashi wahala haka shima yayta bamu wahalar, aka cigaba da yak'in sunk'uri, kowa baya ganin kowa kenan, kwatsam saiga Alhaji Shehu Darma yazo mana da labarin Camera fa Na hannun Alhaji Auwal Fharuk, wannan yasa muka koma bobiyarsa, mun masa tayin dukiya mai yawa sau babu adadi amma yak'i saurarenmu, munma rayuwarsa barazana nanma a banza, daga k'arshe muka nemi kasheshi shima, amma ya tsira bai mutuba, Yarima Sameer ma ya d'aukeshi zuwa India, dukda a India d'inma bawai mun barsa bane, canma musha bibiyarsa da barazana, amma taurin kansa yahanashi bamu har zuwa yau d'inan, munsha kaima rayuwar Sameer hari shima ta 6angarori da dama amma yana shallakewa cikin tsarewar Ubangiji, wannan shine abinda ya faru yamai shari'a”. Babu abinda kakeji a kotunnan sai sauke ajiyar zuciyar jama'a, alk'ali yace yaje ya zauna. Yad'anyi rubuce-rubucensa sannan yace “kotu tana buk'atar son ganin Waziri a gabanta”. Waziri Munafuki, saikace an tsamo 6era a ruwa haka yafito yana wani kakkange fusaka, shima inda kowa ke tsayuwa yaje ya tsaya, bayan ya fad'i sunansa Alk'ali ya jeho masa tambaya. “humm Waziri, kotu zataso sanin minene ya had'aka da Sarki Saifudden da zafi haka? Harka za6i cutar dashi wajen had'akar wasu bare can?”. Waziri yakuma k'asa da kansa, murya a raunane yace, “maganar gaskiya son zuciyane kawai ba wani abuba, danshi mai martaba ya kasance mutum mai zama akan ra'ayinsa, sannan mai gaskiya da sauk'in hali, nikuma nacika tsugunne-tsugunnen rashin gaskiya, sannan inada sonkai, komai nafison a masarautar gagara badau a fifitani saman kowa, akuma girmamani, wannan halin nawa nason handame komai Na mutane yasaka kullum Sarki kemin nasiha dason gyara halayyata, nikuma nak'i saurarensa, saina kallon hakan danake matsayin cin zarafina yakeyi a kullum, lokacin dana fara ganin take-taken Sarki nason tu6eni sai hankalina ya tashi, nafara Neman mafita, (kusan dai ita sarautar waziri ba gadonta akeba a k'asar Hausa) ina cikin fad'i tashine Neman mafitane wad'annan turawa biyu su Mike sukazo min da tayin mak'udan kud'i da wasu alk'awura, bisa sharad'in sonjin sirrin masarautar gagara badau, babu wani 6oye-6oye Na sanar musu komai, karaf sai'a kunnen wani dogari amintacce ga Sarki, shine yaje ya sanar masa komai, Sarki yakirani har turakarsa ya titsiyeni, yaci mutuncina iyakar iyawarsa, wannan Abu shine ya fusatani, naje Na samu su tanderu muka had'e, dan aganina Sarki ya tozartani a masarauta, tunda gashi yana niyar tu6eni kamar yanda ya fad'amin, nikuma aganina kafin ya tu6eni ya tozartani gara ni nahad'a kai da wad'anda zamu tu6eshi, wannan dalilinne yasakani basu had'inkai, akuma washe garin dana amso allurarna da asuba muna salla, anyi sujudar farko ta sallar asubahi Na kafa masa allurar a cinya Na tsiyaye ruwan kafin a d'ago, amma Sarki dukda nasan yaji zafi, yakumasan cutar dashi akeyi baiko motsaba, saida aka idar da sallar dashi, anayin sallama ya juyo muka had'a ido, baisamu damar min maganaba ya yanke jiki ya fad'i, tun daga wannan lokacin yakoma shida gawa banbancinsu kad'annane, to dama shima wazirin Sarki Abdul-Fatah kuma d'an uwansa shima da nashi shiri akan Sarki Saifudden, dan yanajin haushin ba jikokinsa y'ay'an y'arsa gimbiya Marawuyane (mama Fulani) zasuyi mulkiba, dan lokacin su zaharadeen sunyi had'arin jirgi sun mutu, to burinsa kullum ya durk'usar da Sarki Saifudden jikansa Jalaludden ya gaji mulki, wai tunda gimbiya Kahdija matar Sarki Abdul-fatah ta gaje musu masarauta, shima dolene d'iyarsa mama Fulani ta gaje ta gagara badau, wannan ya sakashi shigowa cikin tawagarmu dasu tanderu, Sarki Saifudden Na kwanciya jinya kuwa aka d'ora Jalaludden bisa karaga a matsayin mai ruk'on kwarya, bisa alk'awarin zan cigaba da wazircinsa, sannan kuma sarautar waziri tazama din din din, y'ay'ana ma zasu iya gadona, shiyyasa lokacin da aka sanarmin ga camera a hannun mai dawakai nayi azamar son kar6a, amma yamin gardama, nikuma Na kashesu shida matarsa dan karsu tonamin asiri, nakuma saka yara subimin d'ansa daya gudu da camera, a masarauta kuma nace Badi da kansa ya kashe iyayensa. Maganar gaskiya mama Fulani batasan mahaifinta yayi wannan shirinba, danya ta6a tuntu6arta da batun kashe Sarki Saifudden amma tace Sam bata aminceba, bazata ta6a kisan kaiba, shiyyasa bai ta6a sanar mata yanda akayiba, shikansa Sarki Jalaludden baisan komaiba, dan yana masifar son d'an uwansa, bayason abinda zai ta6ashi, shiyyasa nikuma Na dinga kwantar masa dakai dan karma ya fahimci wani Abu, nasaka d'ana Harun yake bibiyar mana dukkan motsin Sameer. Wannan shine dalilina yamai shari'a”. Alk'ali yace, “toshi mahaifin gimbiya zulfa uwargidan Sarki na yanzu minene ya kawo shi a ciki? tunda dai yanzu bashida k'arfin da zaizo kotu ya bamu amsa saboda girma ya kamashi sosai, nakuma San Kasan komai shima a kansa?”. Waziri ya gyara tsayuwa yana jinjina kai, yace, “shima dai shirinsa bai wuce akan mijin y'arsa yayi sarautar ba, wato Sarki Jalaludden Na yanzu kagadai dolene jikokinsa su gaji sarautar anan gaba, sannan kuma yanajin haushin sarki Saifudden d'in, dan shi yaso ya auri d'iyarsa zulfa amma sai Marigayi Sarki Abubakar ya had'ashi da d'iyar Amininsa gimbiya Zaitun, bayan rasuwarta ma Yakuma masa tayin wata y'ar tashi amma sai aka maye gurbin gimbiya Zaitun da gimbiya Zeenah, shi burinsa dai ya nuna inhar ank'i aurama Sarki mai sarauta y'arsa to jikokinsa koda tsiya saisunyi sarautar gagara badau d'in, lallai wannan dai shine dalilinsa shima”. Babbar magana, wai dukdai akan mulki kayan duniya aketa wannan k'ulla-k'ulla, Wanda gashi yanzu a cikinsu wasuma sunbar duniyar baki d'aya, wannan wace iriyar masiface haka?. Alk'ali ma kasa magana yayi, saida yad'au ruwa yasha tukunna, Galadima kam ai babu mai iya tantance halin dayake ciki, ya kwantar da kansa jikin kujera yasaka handkerchief ya lullu6e fuskarsa gaba d'aya. Alk'ali yace, “Lallai a gaisheku, Ku yanzu dan girman ALLAH bakuji kunyar kankuba? Kamarku manyan mutane da k'asa ke alfahari daku da girmamaku Ashe ru6a66une a bad'ini, maciya amanar k'asa, lallai barin irinku ma ai had'arine wa duniya baki d'aya, dan duk abinda aka nema Na wulak'anta k'asarku zaku iya mik'awa domin cikar burinku, kune masu 6ata shugabanni Na kwarai masu k'yak'yk'yawar zuciya, ALLAH ya cigaba da tona mana asirin irinku a k'asarmu”. Gaba daya Kotu ta amsa da Amin!!!, Alk'ali yay k'asa da kansa yana bincike a k'aton books d'in gabansa kusan hud'u, kotu tayi tsitt kowa ya zuba masa ido, ya d'auki tsawon lokaci yana rubuce-rubuce kusan 30minute's sannan ya d'ago yana cire eyeglasses d'in idonsa, yasaka handkerchief ya goge fuskarsa sanan ya goge eyeglasses d'inma ya maida a idonsa yana kuma gyara zama dayin gyaran murya. Yace, “Bisa ga hujjoji da bayanan da suka fita a bakin wad'anda ake zargi kai tsaye, wannan kotu mai adalci ta yankema wad'annan mutane 20 da sukayi gamayya wajen ciwon Sarki Saifudden hukunci d'aurin rai da rai a gidan kaso, saboda kisa da suka dinga sakawa a nayi bayan laifinda suka aikata”. Kotu ta d'auki sowa gaba d'aya, saida alk'ali ya tsawatar ta hanyar buga gudumarsa, kowa yay tsitt. Alk'ali yacigaba da fad'in “Wazirin Sarki kuwa hukuncinsa shine kisa ta hanyar rataya, sakamakon kisan mai dokuna da matarsa, Hakama Alhaji Shehu darma, d'aurin rai da rai da horo mai tsanani saboda bada had'in kai wajen kisan d'an Uwansa Alhaji Abdul-Hakeem uba, dakuma tsiyatakun da suka dinga sakashi yanayi. Akwai yaransu dake hannu bisa laifi daban-daban da suka sanyasu, suma dai d'aurin rai da rai ne akansu, Irinsu Alhaji Halluru, Timothy da sauran su shekaru 30-30 ne hukuncinsu, da horo mai tsanani, dukansu babu maganar beli, dolene saisun rayu a gidan kaso. Sannan wannan kotu ta wanke Muhammad Sameer Saifudden bisa zargin ta'addancin Garkuwa da yara da yayi, dan bai ta6a kowaba a cikinsu, dagashi har tawagarsa da suka bashi gudunmawa kotu ta wankesu tas. Akwai d'angidan Waziri mai Suna Harun, kotu ta yanke masa zaman kaso Na shekaru goma bisa ga cin dunduniya Muhammad Sameer daya dingayi wajen sato bayanansa, ina fatan kowa yasamu hukunci dai-dai da abinda ya aikata, kuma duniya ta gamsu da hukuncin da muka yanke?”. Kotu ta d'auki sowar gamsuwa da ALLAH wadai da halin irinsu waziri dasu Darma. Kowa tur yakeyi da halin masu. Alk'ali ya buga gudumarsa alamar kotu ta tashi, daganan kowa ya mik'e saida ya shige sannan aka kacame da hayaniya, harda masu kaima su Alhaji Halluru duka, ana musu ihu, saima da aka fidosu mutane sukaita jifansu da duwatsu, sai y'an sanda suka dinga karesu har aka zubasu a mota, wasunsuna kuka sukeyi rurus dan ganin iyalansu ko damuwama basuyiba, wasu a cikin yaransu ai ko'a kwalar rigarsu, k'alilanne a cikinsu suka damu. Galadima har kowa yafita a kotun shi yakasa motsi, saida Abba Hayatudden da baffi da Abban munaya sukazo kansa, baffi ya cire Handkerchief d'in daya lullu6e fuskarsa saisukaga ashema a sume yake?, rikicewa sukayi, aka samo ruwa Abba Hayatudden ya shafa masa a fuska ya kawo numfashi. Zabura yayi, saida Abba Hayatudden ya rungumesa, jinsa a jikin k'anin mahaifinsa saiya saki wani irin kuka maiban tausayi, daga Abba har Baffi suma idonsu yacika da kwalla, Abba Hayatudden yashiga shafa bayan Galadima alamar allashi. Kusan mintuna uku ya d'ago da hanzarinsa yana fad'in “Abba Munaya da Nuren, lallai ban yarda darashin zuwansu kawo camera ba, alamun sarkin mota sun nuna akwai wani abu”. Da sauri baffi ya fita Neman sarkin mota, a waje ya iskeshi tsaye yana jiran fitowar Galadima. Baffi ya tambayesa miya faru, bai 6oye masaba ya sanar dashi komai, hankalin Baffi a tashe yakoma ciki yace su fito suje, hakkanne ya tada hankalin Galadima da tabbatar da lallai akwai matsala. A rikice suka shige mota, ko kallon y'an jarida dakeson jin bayani a bakinsu basuyiba, balle bi takan jama'a dake jiran su fito sumusu jaje....................✍🏻 *_Lallai K'arshen munafuki dama duk inda yake jin kunya, duk yanda kakai ga k'ulla kuttun sharri watan watarana saikaga k'arshenka, a duniya ne kokuwa a lahira, babu abinda ke dawwama sai ALLAH, Idan khairan ka shuka lallai saika girba khairan, idan kuma sharranne shima saika girbe abinka, duk danne Gaskiya da k'arya zatai wlhy watan watarana sai gaskiya tadawo sama k'arya ta koma k'asanta, kwanaki 99 ne suke zama Na masheranci, 1 tak kuma suzama namai gaskiya da k'yak'yk'yawar zuciya, d'ayarnan kuma saikaga yazo maka da nasarorin daka rasa shekaru aru-aru, duk nisan jifa k'asa zai fad'o, gashi dai yau su Harun sunzama a k'asa, k'asanma cikin matuk'ar k'ask'anci, musamman ma iyayensu._* _Ya rabbi ka tsaremu ka tsare mana zukatanmu, ka hanamu cutar da wani koda da fatar bakice, ko'a social media bana fatan kwana da hak'in wani ko hassadar wani, idan nabar duniya wace amsa zanbama ubangiji akan d'aukar zunibin wandama banta6a ganiba a zahiri😭, ya ALLAH ka gafartamana muda iyayenmu da dukkan musulmai baki d'aya, ALLAH ka rabamu dacin hak'k'in kowa koda kwayar zarrane😭😭👏🏻._ _Kumuje zuwa asibiti, danjin wane hali Munaya take ciki itada Nuren kuma?.😔_ *_Nagode sosai da addu'oinku gareni, da mahaifina, ALLAH ya bada ladan zuminci Yakuma kar6a mana baki d'aya, bansan yazan nuna godiyata ga masoyanaba, saidai nace kuma ALLAH ya biya muku buk'atunku, kaini har mak'iyinama ALLAH ya biya masa buk'atarsa ta alkairi, dan saida mak'iyi duniya ke dad'in zama🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀, idan babusu tamkar miyace lami babu gishiri da magi🤨😝😂.🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [8/6, 2:05 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ________________________ *_K'atotuwar gaisuwa a gareku my sweet friends_* _Shamsiyya Yahaya D/Z, Farida Muh'd gadanya (y'ar farida😝), Umma Yahaya /D/Z, Sadiya Abdullahi S.A, Hadiza 'Dayyabu Fama, Bahijja Musa Tyw, Hadiza yakubu Tyw, Fatima 'Dayyabu Fama, Hadiza isyaku Gurun, Hadiza Umar fama, Ummi Sani Tyw, Fa'iza Zakari Tyw, Sadiya Sulaiman SS, Hauwa'u Muhammad Nsw, Nafisa Ibrahim G/mutun 1 (I miss you y'ar gidan baban😅) Rabi'a Lawan Tyw (ho y'ar kwana🤣) Ruk'ayya Muhammad Tyw, Zainab Ado Tyw, Zakiyya Liti Tyw, Sadiya Lawan Fama, Bariya Salisu yashe, Umayya Yusuf R/gado, Zahariyya idris R/gado, Naja'atu Rabi'u R/gado, Zuwaira Abdullahi k/giwa, Nafisa kabir Tuge, Shamsiyya Kabeer Tuge, Zainab Adam Bichi, Amina Rabi'u N/iya, Ummi k/giwa, Maryam Tasi'u Tyw (ALLAH ya gafarta miki, ya raya abinda kika bari😭)._ *Aradun ALLAH yawane daku, wasuma sunansu ya 6acemin😔, I miss you all. Kai duk wadda ma yay GGASS D/ZABUWA ina mik'o gaisuwar fatan alkairi a gareshi, Musamman ma y'an 2010 Graduation boko and Arabic, Alkairin ALLAH yakai gareku baki d'aya. Bilkisa Ibarheem Musa (Bil-Gur) kai malam basheer lamba ya iya sa suna🤣, Na gaisheku irin trillions d'inan wlhy, nasan kunata missing tuwon Malam kabiru da koko mai saka barci, ga fatan wake mai kwari (nama a wancan lokacin🤣😜) Yaya kwad'on tuwo da shayi mai kauri🤸🏻‍♀, kai duniya, komai Na rayuwa labari, INA missing d'an sirri d'ebo ruwa wlhy😔😂.* _________________________ *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣0⃣ .................Galadima ganima yake kamar Sarkin mota baya Sauri, amma baiyi maganaba, zuciyarsa tamafi motar gudu, dan bugawa take da sauri-sauri tamkar zata fito. Suna isowa bai saurari an bud'e masaba ya bud'e da kansa yay cikin asibitin, dayake k'aramin asibitin ne, na kud'i su Ahmad suka kaisu, da sauri Nurses d'in dake reception suka masa sannu, tare da gaisheshi, dan 6atancin da aka musu Shida sh Munaya a wancan lokacin yakuma sakawa wad'anda basu sanshiba ma suka sanshi, ga kuma abinda ya faru a kwanakinnan. Uffan baice da suba yay gaba abinshi, cikin takunnan nasa Na k'asaita da izza, Wanda a yanzu yak'ara armashi da 6acin rai. Su Ahmad da suka hango tahowarsa duk suka mik'e a tare suma suka nufosa, kallon mamaki yake binsu dashi, suma duksun lura da hakan. Gebiral yace, “Uncle!”. Kallonsa Galadima yayi idonsa sakaye cikin eyeglasses daya 6oye jajayen idonsa, kafin wani ya sake rmagana a cikinsu doctor ya iso wajen, duk hankalin su suka maida ga doctor d'in suna tambayar ya jikin Aunty?. Doctor yace, “ku kwantar da hankalinku, insha ALLAH komai zai zama normal, Ranka ya dad'e barka da zuwa”. Hannu kawai Galadima ya iya d'aga masa, a lokacinne suma su Abba Hayatudden suka k'araso wajen. A hankali Galadima ya bud'e baki yace, “Ina matata da d'an uwana?”. Cikin girmamawa Doctor yace, “Ranka ya dad'e inason magana dakai idan babu damuwa”. Kamar Galadima bazaiyi maganaba saikuma ya gyara tsayuwa yana fad'in “Inason ganinsu tukunna”. Doctor yay jimm baice komaiba. Hakanne ya d'arsa tashin hankali a zukatan kowa Na wajen, Galadima ya yunk'uro zaiyi magana doctor yay saurin taresa ta hanyar fad'in “Amma ranka ya dad'e namijin kawai, dan gaskiya ita ba'ason ayi wani kwakwkwaran motsi a kusa da itane”. Kowa Na wajen ajiyar zuciya ya sauke, danjin sunada rai, Galadima daya kasa koda motsi doctor ya kuma kalla, zaiyi magana ya d'aga masa hannu alamar baison jin komai. Abba Hayatudden da Baffi da sukasan halinsa idan yana cikin damuwa suka kalli doctor, baffi yace, “doctor yakamata ko shi kad'aine ya ganta, mu saimu duba Nuridden d'in”. A sanyaye doctor ya gyad'a kai, dan inda sonsamune babu mai shigar. Nurse ya had'a su da ita takaisu inda Nuren yake, amma kar ayi hayaniyar dazai farka, dan ana buk'atar yasamu barci sosai. Doctor kuma yayma Galadima jagora da kansa, amma a k'ofar d'akin suka cire takalmansu, dagasu sai sock's d'in k'afarsu suka shiga. 'Dakine madaidaicine da gad'o d'aya, asibitin sunada Kayan aiki babu laifi, tamkar an zarema Galadima lakar jiki haka yake takawa cikin sand'a, doctor ya nuna masa kujera guda d'aya dake kusa da gadon, idonsa a kanta tunda suka shigo, harya zauba yakasa janyewa, tana kwance sam6al a gadon tamkar wata gawa, kanta nad'e da bandeji alamar taji ciwo akan, dan har fuskarta tanuna saboda kumburi da tayi, alik'a mata oxygen a hanci Wanda da alamar shike taimakawa numfaahinta fita, ya maida kallonsa ga damtsen hannunta da shima yake anad'e, sannan kuma tafin hannunta ma haka, wasu hawaye masu zafi suka gangaro tacikin eyeglasses d'in idonsa daya hana ganin tahowarsu tun daga cikin idon. Ya kalli doctor da shima yake tsaye kansa duk'e a k'asa alamun damuwa, baice komaiba ya mik'e ya fito abinsa, doctor ya biyoshi a baya shima da hanzari. Da hannu yamasa alamar ya kaisa inda Nuren yake. Nanma shine yamasa jagora, duk inda suka gitta idanun mutane akansa, oho baimasan sunayiba, abinda ya dameshi shine gabansa. Su Abba Hayatudden suna d'akin har yanzu, shigowarsu Galadima ya sakasu juyowa suna kallonsa gaba d'aya, ya k'araso gaban gadon idonsa akan Nuren dake barci shima, saidai shi babu bandeji ko d'aya a jikinsa, dan baiji rauniba, dukansa da sukayi a kai ne ya sakashi suma, anama zuwa asibitin babu dad'ewa ya farfad'o, shine sukai masa allurar barci da saka masa k'arin ruwa danya huta, sanda zai farka ya farka da k'arfi a jikinsa.. Galadima ya durk'usa a gaban gadon ya kamo hannun Nuren cikin nasa, yana k'aunar Nuren sosai har cikin ransa, danshi mutumne simple, idan yamaka wani abun bazaka ta6a cewa shi jinin sarauta baneba, ko kad'an bashida damuwa a rayuwarsa, tunba yanzuba Nuren yake bama rayuwarsa gudunmawa, baita6a k'osawa ko gundura da halinsaba, balle yace masa bazaiyiba, saidai inhar abin baida tsarine zai bashi shawaran a canja kokuma ayi haka ko haka.......... Wayarsa datai ring ce ta katse tunaninsa, yad'an karkata yana cirota a aljihun wandon yadinsa, ring d'in daya sakama papi shi kad'aine ya sakashi fahimtar waye, ya mik'e daga gaban gadon yana picking call d'in, saida ya fice a d'akin gaba d'aya sannan ya amsa sallamar da papi yamasa cikeda girmamawa da tsantsar damuwa. Daga can ajiyar zuciya papi yayi, dan baiyi zaton samun Galadima cikin k'oshin lafiya hakaba, cikin tausasa Murya papi yace, “Muhammad kana inane?”. Shiru galadima yayi, kamar bazai iya maganaba, saikuma ya bud'e baki da k'yar yace, “papi asibiti”. “Asibiti kuma? Wanene babu lafiya?”. Kasa danne kukan daya taho masa yayi, ya fice daga cikin asibitin da sauri, mota ya bud'e ya shiga, ya kife kansa a sitiyari ya fashema papi da kuka mai tsima rai da 6argon jiki, gaba d'aya jikin papi yay sanyi lakwas, saima ya kasa magana shima, yay shiru kawai yana sauraren jarumin jikansa mai yawan hak'uri da juriya akan abu, saida yay kusan mintuna biyu yanayi, papi ya tabbatar nauyin da zuciyar galadima tayi ta ragu sai yay gyaran murya, cikin tausasa harshe yace, “Muhammad Sameer mike faruwane? Kokuwa kukan farin cikin cikar burine?”. Da k'yar Galadima ya iya bud'e baki yace, “papi yanzunan duk abinda suka aikata a gareni tsawon shekaru bai ishesuba? Saisunyi yunk'urin kashemin d'an uwana da matata? Papi minayi musu da zaifi haka? Miye laifin mahaifina danyak'i goyama k'arya da cin amana baya? Miye laifinsa danya zama shugaba? Bayan hakan ba shirinsa bane tsarin ALLAH ne? Miyasa suka manta babu abinda ke dawwama sai ALLAH, papi inhar matata ko d'an uwana suka rasa ransu wlhy bazan hak'uraba, saina kashesu da hannuna nima s........” Dakatar dashi papi yay ta hanyar kiran sunansa. Galadima ya amsa masa da k'yar. “Kayi hak'uri Muhammad kaji, ALLAH yana tare da masu hak'uri, Hayatudden ya sanarmin komai, ALLAH yabasu lafiya, ba shari'ar duniya bace kawai shari'a, akwai babba wadda babban alk'ali zaima kowa, koba komai ALLAH ya kunyatasu tun a duniya, kowa yasan misuka aikata, kuma ka dak'ilesu suda masu burin aikata irin nasu, ka ringa tunawa akwai tonon asirin dayafi wannan, harma abinda yafi wannan da suka aikata akwai babbar kotu mai cikeda d'unbin jama'a da babban alk'ali a gaba, banason kabar wannan abin yayma zuciyarka tasiri haryakai ga kadaka k'asa, sannan karna kumajin kayi kuka, ka kwantar da hankalinka muci gaba da musu addu'a, insha ALLAH gobe zan shigo garin”. Gyad'a kai Galadima yayi tamkar yana gabansa, papi yakuma kwantar masa da hankali da nasiha mai ratsa jiki, saida ya tabbatar hankalinsa ya kwanta sannan ya barsa.... Ya jingina da kujerar yanamai lumshe idanu, wata nutsuwa ta musamman Na ratsa jinin jikinsa da zuciyarsa, knocking glass d'in da akayi ya sakashi bud'e idanu a hankali, ganin sarkin motane saiya sauke glass d'in k'asa, cikin girmamawa sarkin mota ya mik'o masa gorar ruwa. Bai musaba ya kar6a yana gyad'a masa kai alamar ya gode. Sosai yasha ruwan kuwa, wata nutsuwa takuma saukar masa, ya kuma d'aukar kamar 5minutes ya fito daga motar, ya koma cikin asibitin, yanson ganawa da doctor d'in, idan yaji bai gamsu da aikinsaba dolene yasan mai yuwuwa. Yana shigowa su Ahmad suka k'araso gareshi suna gaidashi da jajanta masa. Cikin k'arfin hali yace, “baku tafi gida bane?”. Sarkin mota dake tsaye kusa dasu yace, “Ranka ya dad'e ai Ahmad shine ya taimakeni nakawo camera d'in kotu d'azun”. Da mamaki Galadima ya kalli Ahmad yana nunashi da d'an yatsa alamar kaid'in?. Murmushi Ahmad yayi yana gyara tsayuwa. yace, “Uncle bayan fitowa daga kotune za'a hutunnan sai naji wani yaron su Abbana yana waya akan atare su Aunty a kar6a Camera d'in, dan basa buk'atar ta k'araso Court d'in, to hakan danaji shine Na k'arasa garesa Na bigi cikinsa akan zancen”. “nake cemasa zamuje ni da su Ahakam muma a kwato Camera d'in damu, so hakan dayaji saiya d'auka da gaske tare nake dasu, shine yabani key d'in mashin. Ina ajiye driver d'inka, sai mukazo asibiti ni da Yassar muka sanarma da Uncle d'ina, shine ya bimu da Ambulance har wajen da abun ya faru muka d'akkosu”. Galadima ya kamo hannun Ahmad ya rungumesa, yayma su Yassar dake kallonsu alamar suma suzo, cike da farin ciki suma duk sukazo jikinsa. __________________________ Hankalin mai martaba a matuk'ar tashe yake, jin wai dan kawai yayi mulki wasu suka bada gudunmawa domin durk'usar da d'an uwansa, “hazbinallahu wa ni'imal wakil” wannan wace iriyar masiface hakan?. Sai safa da marwa yakeyi a bedroom d'insa, idanunsa Na kwarar da hawayen tausayin d'an uwansa da Galadima, ALLAH Sarki mahaifiyarsa, yadad'e yana zarginta akan ciwon d'an uwansa, Ashe babu hannunta a ciki, son zuciyar mahaifinta ne, Wanda a yanzu haka tsufa ya kamashi sosai. Waya ya d'auka ya kira Abba hayatuddeen danyaji wane hali d'an d'an uwansa yake cikine? Dan yayi tsumayen shigowarsu masarautar amma yaji shiru. Bugu biyu Abba Hayatudden ya d'aga. Mai martaba ya tambayeshi suna inane?. Abba hayatudden ya amsa masa da vewar gasu a cikin asibiti, Dan mutanen su Alhaji Mansur sun saka an tare matar galadima a hanya itada Nuridden yayin kawo Camera Court. Kasa magana mai martaba yayi, saboda jin kuma wani sabon zaluncin, Wanda suka aikata baya baima ishesuba kenan. Abba Hayatudden ma bai kuma cewa komaiba saboda yasan ran yayan nasa ya 6aci. Mama Fulani kanta yau cikin damuwa take, bata ta6a tunanin mahaifinta zai iya aikata hakanba, dukda tsantsar son datake da burin y'ay'anta suyi mulki bazataso duk'usar da Saifudden akan hakanba, shekaru 26 bawan ALLAH Na kwance yana jiyya tamkar gawa, banbancinsa da gawar fitar numfashi, wannan wane irin son zuciyane su jinin sarauta sukeyi? Shikenan saboda sarauta sai aita halaka juna? “Ni Marawuyya wannan wane irin burine mai cutar da imani.......” Lallai zato zunubine koda ya zama gaskiya😢, kiyi hak'uri mama Fulani munata zarginki Ashe ba haka bane🤔🤦🏻‍♀. .............................★ A gidansu Munaya ma hankalinsu a matuk'ar tashe yake, gasu Abdurraheem nata kuka, dan tunda Munaya tabar gidan suke kuka, kukansu ya tada hankalin Munubiya dasu Inna sosai, lokacin da aka harbi Munaya bak'aramar fad'uwa gaban Munubiya tayiba, ta mik'e a zabure tana dafe k'irji, number Munaya tashiga nema, dan taji a jikinta wani mummunan abu ya faru da y'ar uwarta. Lokacin da labarin abinda ya faru da Munayar ya iso garesu mafi yawan jama'ar gidan saida suka koka, Dady kuma ya hana kowa zuwa asibitin, saisu mazan kawai sukai shirin zuwa, gashi basusan wane asibitin bane. __________________________ Iyalan su waziri hankalinsu a matuk'ar tashe yake, hakama su Alhaji Sageer, ga duniya tanata ALLAH wadai dasu, gaba d'aya yau kowacce kafar yad'a labarai da social media maganar kenan, su kansu sauran manyan kowa ya shiga hankalinsa, dan lamarin yayi matuk'ar girgozasu, suna yabama basirar Galadima matuk'a, gashi yabi ta hanyar da babu Wanda yata6a zaton zata 6ille masa yayi nasara, inhar za'a iya samun irinsa a yau, to lallai wataran za'a samo Wanda ya fisa ma. ....................★ Yanda masarautar su Galadima take a harmutse gameda wannan lamari haka tasu papi ma ta gama harmutsewa, dan lamarin ba'a cewa komai, cin amanar da waziransu sukayi yayi matuk'ar girgiza masarautun, bakajin komai sai gutsiri tsomar bayi da dogarai, harma da manyan gidan ba'a barsu a bayaba. Tashin hankalin da papi da inno suke ciki ba'a magana, ga Sauban ya tasasu gaba yanata kukan son zuwa yaga halin da Munaya da Nuren suke ciki, harma da yayansa. Dukda an hana fad'ama Su Momma amma saida labarin yakai musu, aranar aka nemama Aunty Mimi ticket d'in tahowa Nigeria, Samha nata kuka itada Khaleel zasu biyota, amma bata sauraresuba, dan hankalinta a matuk'ar tashe yake. ............................★ Doctor da kansa ya fito yayma Galadima iso cikin office nashi, bayan sun zauna doctor ya kalli Galadima cikin alamun damuwa, yace, “ranka ya dad'e da farko dai ina mai baka hak'uri akan zaluncinsu mijin y'ar uwata, ALLAH yay maka babban samako da sayya agaresu”. Murmuahi kawai Galadima yayi amma baice komaiba. Doctor ya kuma gyara zama yana fad'in “Alhmdllh jikin namijin babu wata babbar matsala, yanzuma mun saka masa alurar barcine cikin ruwan danya huta sosai yasamu nutsuwa, daya farka Normal zaku gansa. Ita kuma akwai harbi da akai mata a hannu, amma Alhadullh mun samu nasarar cire harsashin, tafin hannunta kuma shima anji mata ciwo, dan yatsunta Na tsakkiyama duk sun samu karaya, amma shima an gyarashi, maganar gaskiya ranka ya dad'e bazan 6oye makaba, tasamu buguwa akai, dan ALLAH ne ya tak'aita batasamu wata babbar Matsala a brain ba, saidai ahalin yanzu dukkan wani motsi mai k'arar sauti bama buk'atarsa kusa da ita, insha ALLAH inhar za'a kiyaye cikin kwanaki kad'an komai zai iya dai-daita, takuma dawo normal kamarma komai bai faruba, zamu bata dukkan kulawar daya dace da izinin Ubangiji. daganan har kwanaki uku zuwa hud'u zata kasance a halin barci, dan hakanne kawai zai girmama nutsuwar da muke buk'atar ta samu d'in, kai kad'aine kuma zaka ringa shiga d'akin”. Galadima ya lumshe idonsa tausayin Munaya da yaransu Na kuma mamaye jinin jikinsa da kowanne ga6a, da k'yar ya iya bud'e baki yace, “Doctor! Kana ganin zaku bata dukkan kulawa?. Sannan tanada yara jinjirai, yaya kenan za'ayi?”. Insha ALLAH ALLAH ranka ya dad'e, dan munada kayan aiki a asibitin mu, dakuma kwararrun likitocin da zasu iya aiki a kowacce k'asa, maganar yara inaga inhar akwai mai kulawa dasu acigaba da basu madara har ALLAH yasa ta farfad'o, saboda mu yanzu matsalarmu kawai shine motsin dazai iya farkar da ita ko wanda zaiyi tasiri cikin brain nata”. Gyad'a kai kawai Galadima yayi, yabama doctor hannu sukayi musabaha, daganan ya fito. Kuma ficewa yayi daga cikin asibitin, Sarkin mota yay saurin biyo bayansa, da hannu yamasa alamar yashiga mota suje. Dukda sarkin mota baisan inda suka nufaba haka ya amsa cikin girmamawa. Saida suka fara tafiya ya sanar masa inda zasuje. yana nufi gidansu Munaya dan yaga halin da yaransa suke ciki. Munubiya da kanta ta fito masa dasu itada Ayusher, tausayin su ya kamashi matuk'a, musamman ma Munubiya, dan tayi wujiga-wujiga. Cikin k'arfin hali yace, “kiyi hak'uri Sister, muyi musu addu'a ita kad'ai suke buk'ata a wajenmu, yanzu yaza'ayi dasu Amaturrahman? Dan nakula kamarma yunwa sukeji?”. ‘yay maganar yana kallon yaran da sukayi barcin wahala bayan sun gama shan kuka’. Share hawaye Munubiya tayi. tace, “Yakamata a nemo musu madara, idan kuma Na shayar dasu to shikenan”. Galadima ya jinjina kansa yana fad'in “Bamusan hikimar da ALLAH ya 6oyeba a gaba, karmuyi ganganci, bara kawai a nemo madarar, dan dolene su kwana anan, ita ba'ason mata hayaniya yanzun, maybe ma harnan da wasu kwanaki, saboda ta bugu a kanta, kuskuren kwakwkwaran motsi zai iya shafar brain nata”. Munubiya takuma fashewa da kukan tausayin y'ar uwarta, hakama Ayusher, shi kansa Galadima dauriya kawai yakeyi, danma ya 6oye idanunsa cikin eyeglasses shiyyasa basa ganin nasa tsantsar damuwar. Muftahu ya kira ya sanar masa a samoma su Abdurraheem Madarar da zasu ringa sha. Daga nan gidan yabaro akan cewar Muftahu zai kawo, yakuma rok'esu akan Abdurraheem, dan ba'ason yacika yawan kuka. A gurguje please😏😜 ___________________________ *BAYAN KWANAKI UKU* A kwanaki ukunnan fad'ar tashin hankalin da bayin ALLAH suke ciki 6ata lokacine, musamman ma Galadima da har wata uwar rama yayi lokaci d'aya, hakama Munubiya da innarsu, Nuren dai ya farka tun washe garin faruwar lamarin, kuma jikinsa Alhmdllh yanata murmurewa, saidai tausayin d'an uwansa daya addabi ransa. Ko abinci Galadima bayasonci, sai Aunty Mimi ta turkesa tana bashi abaki, shima baifi yay lauma biyarba yace ya k'oshi. tayi-tayi kuma ya kafe, garama idan tea ne, shima sai an had'a da lallashi, babu abinda ke addabar ransa irin damuwar Munaya da yaransa, sukansu duksun rame, danma suna samun tsantsar kulawane ta kowanne fanni. Papi yazo ya dubasu, hakama su mom da iyayen su Nuren d'in da y'an uwansa, mai martaba ma da daddare yazo cikin 6adda kama ya dubasu. Mama Fulani ma kullum saitazo, a matan Sarki gimbiya Zulfah Ce kawai batazoba, Dan kunyama ta hanata walwala gaba d'aya a masarautar, Mai martaba kuwa ya hanata hanyar ganinsa gaba d'aya itada y'ay'anta, sai matawalle kawai daya nuna damuwa akan abinda kakansu da mahaifiyarsu suka bada gudunmawa wajen aikatawa wan mahaifinsa, sanan yay ALLAH wadai akan son zuciyarsu, koda yaushe yana tare da Galadima da Muftahu a asibitin, da wata buk'ata ta taso kafin Galadima yayi shi yayita. A koda yaushe Momma cikin kira take taji yaya jikinsu Munaya, koda wasa ba'a sanarma Abie komaiba, Dan ana ganin cigaba da haske game da jikinsa sosai, ba'a fatan wani abinda zai maido da hannun agogo baya game da ciwon nasa. Addu'oi kam sosai aka duk'ufa yinsu game da Munaya, wadda har yanzu Galadima ne kawai keda alhakin shiga ya dubata, shima sau d'aya a rana kawai, yau dai duk ake saka ran farkowarta, Dan an dakata damata dukkan wata allura dake sakata barci, saidai kuma har dare babu wani bayani. Zasu tayar da hankalinsu doctor yace suyi hak'uri, maybe zuwa dare ko safiyar gobe ta farka d'in, danba a sume takeba, barcine kawai da sune suka sakata ta hanyar mata allurar. Badan hankalin nasu ya kwantaba sukai shirun, har lokacin barinsu asibitin yayi babu wani bayani game da farkawar tata. *Washe gari*. Duk dai yanda akaso farkawar Munaya a ranar sai a washe garine ALLAH ya amince da hakan, Alhmdllh anci nasarar farkawar tata yanda ake buk'ata, saidai ciwukan jikinta a halin yanzu. Saida doctors suka gama dukkan kai kawonsu naganin komai ya ida daidaita sannan aka bama Galadima damar shiga. Tamkar mai sand'a haka ya shiga d'akin, tana kwance amma idonta biyu, sai dai a lumshe suke, an kuma cire mata bandejin da aka zagaye mata fuska, sai kad'an aka bari inda ciwon yake. Durk'usawa yay a gaban gadon, ya kamo hannunta Na haggu dakeda lafiya ya saka nashi ciki, a hankali ta bud'e idanunta saboda jin tattausan hannunsa cikin nata, ga k'amshin turarensa daya mamaye d'akin Wanda ya tabbatar mata da shid'inne, tana shak'a a hankali. Idonta ta saka cikin nasa, kowanne yakasa koda kwakwkwaran motsi tsawon mintuna 2, a hankali Galadima ya bud'e baki tamkar mai rad'a ko gudun wani ya jisu yace, “Munaayaa I love you, I really love you, I love you more and more my Heartbeat..” Lumshe idanu Munaya tayi, wasu hawaye suka gangaro daga cikin idanu zuwa gefen kunnuwanta, zuciyarta sai wani irin bugawa take da sauri-sauri, ta kuma damk'e hannunsa cikin nata tana maijin tsigar jikinta Na tashi, jininta sai yamutsawa yake a kowanne 6angare. Kuma bud'e idon tayi a kansa, suka sakarma juna lallausan murmushi ga hawaye Na zuba a idonta har yanzu, shima kwalla sun tarar masa a cikin ido sun saka idon wani k'yalli Na musamman daya kuma sakama munaya wata kasala da tsantsar k'aunarsa, ya lumshe idanunsa alamar tabbatar da abinda ya fad'a mata har cikin ransane ba iya fatar bakiba. Itama hawayen ta kuma matsowa, ta bud'e baki da k'yar tana cigaba da kwararo hawaye. Tace, “i love you too yalla6ai, I love you so much...”. ‘takai k'arshen maganar wani kukan Na kwace mata. Hannunta dake rik'e cikin nasa ya sumbata yanamai jin farin ciki, yace, “ki kasance dani Munaya, ki kasance dani har k'arshen rayuwata, ke Katanga tace, haskena ce, farinciki nace, duniyata ce, duk duniya kece mace ta farko bayan mahaifiyata da y'ar uwata danakema so Na musamman, please karki barni uwar y'ay'ana, karki gujeni komai rintsi, nima namiki alk'awarin kasantuwar mu tare har k'arshen numfashi, ki rayu dani, ki mutu dani bugun zuciyata, kamar yanda nima burina kenan a gareki tsawon lokaci”. Lallai yau daba'a halin ciwo takeba har rawa sai tayi, Wanda bata ta6a tsammani ko tunanin zaisotaba shine yake furta wad'annan dad'ad'an kalamin agareta, shine yake rok'onta ta kasance dashi har k'arshen rayuwarsa?, shine yake kiranta katangarsa?, harskensa, bugun zuciyarsa? Koda a yau tabar duniya ta ribantu da nasarorin masu yawan da wahalar k'ididdiga wajen lissafi. Galadima dake share mata hawaye da hannayensa ya duk'a ya manna mata kiss a goshi da saman la66a. Ta kuma bud'e idonta da suke jajur akansa, murmushi suka kuma sakarma juna, ya girgiza mata kansa alamar tabar kukan, idanunta ta lumshe alamar amsawa. Shikam ya tsura mata idanu ko k'yaftawa bayayi, y'ar ramar da tayi saiya k'ara mata k'yau da k'uruciya, ya shafa k'ananun kitson dake kanta ta kuma bud'e ido tana kallonsa. Cikin d'age gira d'aya yace, “baki tambayi ina yaraba?”. Lallausan murmushi ta kuma sakar masa, ta kwanto hannunsa dake sark'e da nata saitin bakinta ta sumbata, sannan ta d'orasa a saman k'irjinta. Tausayinta ya kamashi sosai, domin jikinta akwai zafi har yanzu, ga abincinsu sunyi matuk'ar cika, Wanda zazza6in nata yanada nasaba da rashinsu gareta, dukda akwai Na zafin ciwo. Hakan da tayi shima saiya fahimci mitake nufi, kuma duk'owa yay ya sumbaci goshinta, zaiyi magana doctor ya shigo. Shiru Galadima yay ya juyo yana kallonsa, itama Munaya daga kwancen take kallon doctor ta k'asan ido. Doctor dake gulma da zuciyarsa yana fad'in lallai ya yarda, duk sarautar Sarki a gaban matarsa bawane, matarce ke zama sarauniya..... (Ga naku Matan kwarai sarakin duniya👍🏻👌🏻😜) Galadima ya katse tunaninsa ta hanyar buga yatsunsa biyu suka bada sautin d'as-d'as. Doctor ya dawo hayyacinsa a kunyace. Yace, “sorry ranka ya dad'e, dama Nurse zata goge mata jikine da kuma gasa mata, Dan tasamu sauk'in nauyin da yay mata”. Murmusawa Galadima yay, ya zare hannunsa daga cikin Na Munaya yana mik'ewa tsaye, hannayensa ya hard'e a k'irji yana kallon doctor da fad'in “Doctor da raina zan bar wasu ganarmin sirrina? Ku kawo kayan buk'ata kawai”. Doctor daya fahimci Inda zancen Galadima ya nufa saiya murmusa yana cewa “Afuwan ranka ya dad'e”. Hannu kawai Galadima ya d'aga masa, ya juyo suka had'a ido da Munaya ya d'aga mata gira da cizar lips d'insa. Baki ta tunzuro masa tana yamutse fuska. Ya d'aga kafad'a da ta6e baki alamar bashida matsala🤷🏿‍♂🤣. Nurses biyu suka shigo da dukkan abinda ake buk'ata, Galadima Na tsaye ko kallon inda suke baiyiba, idonsa nakan matarsa k'yam, sukam sai satar kallonsa sukeyi, suka ajiye suna fad'in “Gashi Ranka ya dad'e”. hannu kawai ya d'aga musu amma ko tari baiyiba. Fita saukai cikin takaici, dan sunso yayi musu magana koda sau d'aya ne. Takawa yay a hankali jikin k'ofar ya Mirza key, sannan ya dawo yana cire link d'in hannun rigar farar shaddarsa da tattarewa zuwa sama. Suka had'a ido da Munaya tai azamar janyewa cike da kunya. Murmushin gefen baki yayi yana zama bakin gadon kusa da k'ugumta. Bottoms d'in jikin green d'in rigar asibitin yafara cirewa a hankali, itadai kunya ta hanata bud'e ido, gashi ya tsareta da idanu, Dan tanajin yanda idanunsa ke yawo cikin jininta, salon daya koma wajen cire bottoms d'in ya sakata dafe hannunsa da hannun haggunta, ta bud'e ido tana kwa6e fuska. Gira ya d'aga mata, da wani mata salo da kwayar ido. Babu shiri ta maida idonta ta rufe ruf, tsigar jikinta Na tashi. A haka dai aka gama cire rigar, yaja bedsheet d'in da ake lullu6a mata a k'afafu ya rufa mata a jiki, sannan ya kuma gyara hannun rigarsa yana tsoma madaidaicin towel d'in cikin ruwan d'umin dake a boket, ya matsa dukda akwai d'an zafi ruwan haka yafara danna mata jiki dashi. Tanajin zafi, amma kuma tanajin dad'in d'umin ruwan sosai, k'in yarda tayi su had'a ido har aka gama, ya d'auki wani d'an kwalba da mai ke ciki tamkar zaitun, karantawa yay yaga amfaninsa sannan ya zuba a tafin hannunsa yana murzawa, kumajin tattausan hannunsa daya had'u da sul6in mai tayi a k'afafunta, tad'an kuma bud'e ido tana kallonsa. Ganin ba ita yake kalloba saita shagala da kallonsa, babban mutum mai daraja jinin mulki yau shine ke mata hidima irin haka, itako badan kar ace tayi alfahari ba da cika baki da yawa da tace ta more fiye da kowacce mace (🙄nidai fa bandani, reader's Ku kun yarda harda Ku🤷🏻‍♀)?. Sosai tafara jin dad'in tausar, Dan da salon nutsuwa yake mata, tuni tafara lumshe idanu, hardai barcin yaci galaba a kanta. Sai dai saukar numfashinta yaji a hankali. Ya kalleta yana murmushi da lumshe idanu, bai bartaba saida ya tabbatar barcin yayi nisa, cikin dabara ya canja mata rigar da suka sakko a kayan domin canji. Ya duk'o ya sumbaci goshinta da bakinta yanajan bedsheets d'in sosai ya kuma lullu6a mata. Kayan ya maida gefe, ya koma saman kujerar dake gefem gadon ya zauna ya zuba mata idanu, kai kace yaune ya fara ganinta, ya dad'e a haka kafin ya d'auka wayarsa yana dannawa. A haka Nurses d'in suka masa Knocking, izinin shigowa yabasu, amma sai suka murd'a k'ofar a rufe. K'aramin tsaki yaja yana muk'ewa, shi yama manta ya rufe. Bud'ewa yay yadawo ya zauna yana d'ora k'afa d'aga kan d'aya da kuma d'aure fuska. Tuni Nurses d'in suka shiga hankalinsu, cikin risinawa d'aya tamasa bayanin zasu canjama Munaya bandejin jikinta ne. Batareda ya kallesuba yace, “kuyi a hankali, Dan barci takeyi, idan kuma kunsan zata iya farkawa kubarsa saita tashi ”. Kallon juna suka, kowacce tad'an ta6e baki, d'ayar tace, “insha ALLAHU bazata tashiba ranka ya dad'e”. Nanma Kansa kawai ya jinjina musu yacigaba da latsa wayarsa. Haka sukai wannan aiki a gabansa Dan yak'i fita, data motsa ya zuba musu uwar harara mai rikita hanjin ciki. Dolensu suka bita a sannu har suka samu kammalawa lafiya, kowacce ta fice a tsorace.............✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣1⃣ .................Kusan mintuna 7 da fitar Nurses d'in doctor yay Knocking, Galadima ya amsa ba tare da ya ajiye wayarba, doctor ya shigo abinsa, Nurse d'aya da sukai akin d'azun Na biye dashi. Galadima ya d'ago yana kallonsu fuska babu walwala, Dan shifa yafara gajiya da wannan shigi da ficin, amma baice komaiba. Doctor daya d'an tsargu yace, “Afuwan ranka ya dad'e, dama ina ganin yakamata tafara cin abincine, Dan ruwan da muke saka matane dama yake taimaka mata, to yanzu kuma zata fara shan magunguna insha ALLAH”. Galadima yad'an sauke numfashi yana fad'in “ok, to amma yaranfa? za'a iya kawosu yanzu?”. “eh to, sunkai nawa?”. Yatsu uku Galadima ya d'agama doctor, dukda yayi mamaki saiya danne abinsa, musamman dayaga munayar y'ar k'arama da ita. yace, “Ranka ya dad'e dadai and'an k'ara mana lokaci koda kwana biyune, har yanzu zancen danake maka ba'ason abinda zai cika mata hayaniya a kai”. Jinjina kai Galadima yayi kawai, alamar gamsuwa. Daganan Doctor yay d'an dube-dubensa ya bama Galadima Drugs d'in Munayar akan Nurse zata dinga zuwa tana bata kullum. Doctor Na fita shima ya ajiye wayarsa kusa da ita ya fito, d'akin da Nuren yake ya shiga, yana zaune Aunty Mimi Na bashi abinci a baki, Galadima yad'an hararesa yana fad'in “k'aton banza kacika shagwa6a”. “Uhmyim” Nuren ya fad'a yana ta6e baki da rama Harar da Galadima ya masa. Ita dai aunty Mimi murmushi kawai take da wannan rigima tasu dabata k'arewa, dama can inhar Nuren da Galadima Na waje sai kayi dariya, Dan kafin su rabu sai anyi kusan fad'a goma. Galadima yace, “Ya jikin?”. “Aini kam Alhmdllh, yanzu kawai maganar gaskiya amin aure, inda Na mutufa shikenan, kukan kwana uku zakuyi a wuce wajen, amma in mat......” Hannu Galadima yakai zai bige bakinsa, yay saurin duk'ewa, Aunty Mimi ta sanya dariya, Galadima kuwa kwafa yay yana kallon Aunty Mimi, “oh ALLAH, maimakon kimasa fad'a dariyama kike masa? Wannan yaron wlhy fitsararrene, idan kunk'i masa aurenan zai iya zuwa yayi baku saniba ma”. Nuren ya gyara zama yana hararsa, “Yo angaya maka ni irinkane, soyyaya Na cin zuciyata k'asaita ta hanani fad'e, Malam mufa dama munsan komai, munzuba idone muga yanda wasan zai k'are”. Murmushin da Galadima bai niyyar yibane ya su6uce masa, ya mik'e da fad'in, “Duk iskancin da kamin ninaso, tunda nine nazo dubaka, idan nakuma zuwa d'akinnan kace ba sunanka Nureddin ba”. “Ahaf, yo dama sunana Sameer ne?”. Galadima bai kulashiba, ya kalli aunty Mimi daketa musu dariya, “Auntyna yakamata a sanarma gidansu ta farka, naga har yanzu babu Wanda ya iso”. Murmushi Aunty Mimi ta masa, ta ajiye plate d'in datake bama Nuren Abinci tana cewa, “babu damuwa, mu barsu har zuwa yammar, tunda kaga har yau basu bada damar a shigaba”. “Ok, hakan yayi”. Harzai fice aunty Mimi tai saurin cewa “Abincinfa?”. Kansa ya girgiza mata yay ficewarsa. Nuren dake murmushi ya kalli Aunty Mimi yana fad'in “Auntynmu soyayya nacin Guy d'inan yak'i fahimta”. Dariya tayi “Nuren kenan, ingaya maka sarai yasan yana sonta, shegen son girma da miskilancine kecinsa, amma ai naga alamar yanzu an wuce wajan”. “A haba? Aunty da gaske?”. “kwarai ma kuwa Nureddin”. Hannu yabata suka tafa, yanajin wani sanyi a ransa, da sakama Muftahu albarka a zuciyarsa, danya zama aboki kuma d'an uwa Na k'warai. Fitowar Galadima yaci karo dasu Yassar, ya fad'ad'a murmushinsa, shima yaran sun shiga ransa sosai, k'arasowa sukai gareshi, cikin girmamawa duk suka gaisheshi, ya amsa da kulawa. “ku bakwa gajiya da yawo?”. Soshe-soshen kunya suka farayi, Marcel yace, “ai daga gida muke, munzo muk'ara ganin jikin Aunty da Uncle ne”. Galadima yad'an murmusa yana tura hannayensa duka a aljihu, cikin d'an lumshe ido yace, “kushiga to kugansa”. “Uncle! Auntynfa? Ta farka itama?”. ‘Ahakam ne mai maganar’ Galadima ya jinjina kai. Yace, “ta farka Ahakam, amma tana barcine”. Gaba d'ayansu farin cikine ya bayyana a fuskokinsu, kai kace y'ar uwarsuce ta jini, da wannan farin cikin suka shiga d'akin da Nuren yake, shikuma yakoma inda Munaya take murmushi d'auke a fuskarsa. Dad'an hanzarinsa ya k'arasa gareta, ganin ta farka, zama yay a kujerar suna kallon juna, murya a sanyaye yace, “Kin tashi?”. Da idanu ta amsashi. Ya shafa kanta yana fad'in “Sannu, yanzu ina ke miki ciwo?”. Fuska ta d'an yatsine, ta nuna masa hannunta da kanta. Cikin tausayawa Yakuma mata sorry, sannan yace, “mizaki ci?”. Kanta ta girgiza masa alamar babu komai. Ya d'an 6ata fuska yana fad'in “Ban yarda ba, kinga kuwa yanda kika rame?”. Murmusawa tayi, itama ta masa alamar wai ya rame shima. Baki yad'an ta6e, amma baice komaiba ya d'auka wayarsa dake kusa da ita yay kiran Muftahu akan abinda za'a kawoma Munayar kozata d'anci. Itadai kallonsa kawai takeyi. Ya yanke wayar yana kallonta shima da d'age mata gira d'aya alamar kallonfa?. Dukda taji kunya saita yamutse fuska irin miye abin kallon anan. Galadima yay wani miskilin murmushi cikin murya k'asa-k'asa yace, “Really?”. Ta lumshe idonta alamun tabbabatarwa. “zaki maimaitamin idan kin warke yarinya”. Yay maganar da wata siga harda cije lips. Munaya ta kauda idonta tamkarma bata fahimci ina ya dosa ba. A ranardai haka kowa ya yini cikin farincikin farfad'owar Munaya, gashi anbarsun sunshi sun gagganta, saidai anata musu gargad'in banda hayaniya, tausayin ta duk ya kamasu. Innaro harda hawayenta, aka saka bakin Zane ana sharewa da jemasu Alhaji balala ALLAH ya isa, harda cewa sai an koma kotu an sake sabuwar shari'a an kar6oma jikarta hak'inta. Shi Galadima ma abin dariya ya bashi matuk'a, yadai had'iye yana duk'ar da kai baiyiba, wannan tsohuwa akwai abin dariya wlhy. Munubiya kam rungumeta tayi taita hawaye, itama Munayar nayin nata. ★★★★★★***★★★★★★ Bayan kwana hud'u da farfad'owar Munaya jikinta yayi k'yau Alhmdllh, Dan tana samun kulawa ta kowanne 6angare, ciwukan jikinta ne kawai basu gama warkewaba. Aunty Mimi da Laraba na a d'akin, Dan kowa ya tafi, suna zaune d'auke da su Abdurraheem da ake kawowa su yini yanzu, sai dare a koma dasu. Munaya tana zaune ne a gadon datake jiyya an saka mata filo ta jingina, abincin da aka zuba mata taketa faman jujjuya cokali a cikinsa, tasaba kullum Galadima ke bata abincin, gashi yau tun safe da'aka kirashi ya fita bai sake dawowa asibitinba har yanzu, dukta damu, da taji motsin tahowa za'a shigo d'akin saita zata shine, sai anshigo taga bashi bane sai haushi ya kamata, Munubiya data fahimceta tsaf taita gumtse dariya har suka tafi, su Aunty Mimi hankalinsu gaba d'aya yanaga yaran, basusan mitakeyiba. Turo k'ofar da akayi ya sakasu kallon k'ofar gaba d'aya, dan k'amshin turarensa yafara musu sallama kafin shigowarsa, wayace manne a kunnensa yana magana a hankali, hannunsa d'aya cikin wandon aljihun Ash color d'in shaddarsa daketa maik'o, Munaya daketa sauke k'ananun ajiyar zuciya tunda taji k'amshinsa tad'an saci kallonsa, shima idonsa a kanta, gira ya d'aga mata, tai saurin janye idonta tana tura baki kad'an. Murmushi yayi ya zauna a bakin gadon kusada k'afafunta yana cigaba da wayarsa, yayinda yakema Amaturrahman da aka kwantar kusada ita wasa, yaran sund'an fara wayo, Dan idanuwa k'yar suyita kalle-kalle, kwanakinnan da suka dawo shan nono sunyi y'an k'u6ul-ku6ul dasu abin sha'awa. Munaya dai tafara tura abincin da k'yar, sai wani faman had'e rai takeyi, shidai Galadima dariya na cinsa a rai amma baiyiba, saidai ya saci kallonta ya maida idonsa ga Amaturrahman data rik'e d'an yatsansa gam daya saka a d'an hannunta, kaikace tasan minene. Sudai Su aunty Mimi da laraba suna cigaba da hirarsu, Dan laraba na bata labarin halinda su Abdurrahman suka shiga a kwanakin da Munaya bata farfad'oba ne. Galadima ya ajiye wayar yana d'aukar Amaturrahman da fad'in, “O my lil princess I miss you”. Ya k'are maganar da sumbatar kumatunta, sannan ya juyo suka gaisa dasu aunty Mimi dake kallonsa shida babyn tashi abin sha'awa. Cikin tsokana aunty Mimi tace, “Ai dama shirin kiranka nake danna kula my k'anwa bazataci abincin nanba sai kana kusa”. Galadima ya juya yana kallon Munaya data waro ido tanajan mayafi ta rude fuska Dan kunya, dama aunty Mimi suna kula da ita kenan, itakam taga idi. Galadima yace, “A lallai Aunty Mimi da gaskiyarki fa, kamarma kuka tayi?”. “kad'an dai ya rage tayishi my k'ani, tun d'azun ina lura da ita, rabin hankalinta naga k'ofa”. Laraba da Galadima sukayi dariya, ya kuma kallon Munaya data kasa d'ago kai ta kallesu. Galadima ya had'iye dariyar dake Neman kufce masa, ya ajiye Amaturrahman d'in yana matsowa kusa da ita, Murya k'asa-k'asa yanda su Aunty Mimi bazasujiba yace, “Any problems my Princess?”. Munaya ta saci kallon su Aunty mimi, ganin basa ganinta saita tura masa baki kad'an tana matso k'ananun hawaye. “O my God”. ‘ya fad'a a hankali yana d'ora tattausan hannunsa saman nata, cikin wani salon daya saka tsigar jikinta tashi ya kar6ar spoon d'in. Babu shiri ta sakar masa. Yakuma k'asa da murya yana d'ebo abincin da fad'in, “nifa kibarmin shagwa6arnan kokuma humm”. ‘ya k'are maganar da ciza lips yana jifanta da wani kallon mai cike da sirrika’. Waro idanu Munaya tayi tana kallonsa baki bud'e. Abincin ya zuba mata yana kashe mata ido d'aya. Kunya ta kamata, Dan wlhy Galadima bashida kunya ko kad'an, kad'an daga aikinsa ya aikata duk abinda yazo masa a rai d'in, danta San halin kayanta sarai. bata k'ara yarda sun had'a idoba har yagama bata abincin, ya d'akko d'an Basket d'in da drugs d'inta ke ciki yana dubawa. Aunty Mimi data kasa hak'uri ta mik'e tana tawa, “Oh ni Haneefa, dama abinda ya hanaki cin abincin kenan da gaske dai tun d'azu kiketa cuna baki my k'anwa”. Munaya tai saurin jan d'an gyalen dake yane bisa kanta ta rufe fuska saboda kunya dataji, Aunty Mimi ma akwai iya 6aro zance, kuma ta Fiske abinta. Laraba tayi y'ar dariya itama tana bin bayan Aunty Mimi suka fice, itakam dai birgeta sukeyi sosai, komai nasu a nutse. Galadima dake binsu da murmushi ya juyo da kallonsa ga Munaya yana fad'in, “Saiki bud'e fuskar, dama haka kikeso su fita a barki daga ke sai mijinki ko?”. Babu shiri Munaya ta janye mayafin tana d'an hararsa da kwa6e fuska tamkar zati kuka. Ya ta6e baki da d'aukar ruwa ya zuba a cup yana mik'a mata, kauda kanta tayi gefe kamar bata ganshiba. Mik'ewa yay ya koma kusada ita sosai yana sakata jikinsa, “Haba dai yalla6iyan yalla6ai miye na fushin to?”. Munaya ta ture fuskarsa tana fad'in “Ni babu ruwana dakai, ka koma inda ka fito”. Yace, “Oh God Babie na sorry kinji, wani babban uzirine ya rik'eni, yanzu dai ga maganin kisha, sai amin hukuncin laifina”. Munaya ta matso hawaye sannan ta bud'e bakin ya zuba mata maganin ya bata ruwan tashanye, yakuma zuba wani, ahakadai tagama sha. Dawowa yay tagabanta ya zauna yana murmushi, “Dad'ina dake shagwa6a, amin murmushin mana”. Kauda kai Munaya tayi gefe murmushi na kufce mata. Galadima ya dawo da fuskarta suna kallon juna, cikin k'ank'ance idanu yace, “ko kefa sweedy na, kindai hak'ura ko?”. Kaita jinjina masa tana wani far da ido. Hannunta mai lafiyar ya sumbata, yace, “Thanks My Queen, Saura wanka ko?”. Munaya tai k'asa dakai saboda kunya, danta zata ya manta da maganar wankan da Doctor yace tafarayi yau indai zata iya. Murmushi Galadima yayi, dan kunyar tata na sakashi a shauk'i. Kanta a duk'e tace, “Nidai kabarni zan iyayifa da kaina wlhy”. Baice uffanba ya mik'e zuwa k'ofar ya saka key, yazo yawuce cikin bayin dake a d'akin. A sace ta bishi da kallo harya shige, ta lumshe idonta wani farinciki nabin sassan jikinta. tsaf bayin yake, dan kullum cikin gyaranshi ake, hakama kayan ammafani irinsu boket, buta da sauransu komai need yake, ruwa ya saka danya d'anyi zafi dayake akwai wuta, ya fito yabarshi. Har yanzu idon munaya a rufe suke. Saukar Numfashin Galadima da k'amshin turarensa kawai taji a kan fuskarta, ta bud'e ido da sauri, Ashe yana gab da ita, motsawar datayi saiyazama kawai fuskarsu ta manne da juna, hakan yabashi damar aikata yanda yaso cikin sauk'i. Batada za6in daya wuce mik'a masa ragama gaba d'aya, danya cancanci abindama yafi haka a gareta. Tsawon mintuna biyu ya d'ago suna kallon juna, kasa daurewa Munaya tayi ta rufe idonta, yay murmushi gefen baki yana hura mata iska a saman idon. Dole na bud'e idona nakuma sakasu cikin nasa, a hankali ya furta “I love you so much my Munaah”. Murmushi na masa mai kashe ga66an jiki, na matsa kad'an ina bashi Sumba a kumatu, lumshe idonsa yayi yana sauke wani nannauyan numfashi, ya d'ora kaina a k'irjinsa, daddad'an k'amshin turarensa ya shige hancina, nima na lumshe idanu ina shak'a da godema ALLAH. muduka nutsuwa ta musamman ta sauka a zuciyoyinmu. Wayata datai ring ce ya sani d'agowa daga jikinsa na zauna sosai ina kauda fuska saboda kunyarsa. Ganin Samha Ce na d'aga wayar cikeda farin ciki. Galadima mik'ewa yay shima ya lek'a ruwan daya saka, ganin yayi zafi saiya kashe ya juye, surkawa yay, saida yaji yayi dai-dai sannan ya fito yana cire bottoms d'in rigar shaddarsa, hankalin Munaya baya garesa, shiyyasa batasan miyakeyiba, sai ji kawai tayi an amshe wayar tareda yin sama da ita. Da farko ma tsorata tayi, zata saka masa ihu yay saurin cemata “Shiiiii!!”. Ajiyar zuciya na sauke na kallesa, ya kashemin ido d'aya. Murmusawa nayi ina janye idona daga kallonsa, dan naga lamarin nasa na Neman fin k'arfina, koya manta a ina muke oho? harda su cire rigafa. Nidai wannan wanka anyisane kawai dan banida yanda zanyi, dan dana nema yin gardama saiya had'e fuska yana hararata, dole nabarsa yayi yanda yakeso, ya d'auramin towel ya kamo hannuna muka fito, Muduka Kallon Amaturrahman mukai daketa wutsil-wutsil da k'afafu. Na zauna a bakin gadon shikuma ya jawo kujera ya zauna yana rik'o hannuna mai ciwo, fara'ar dake a fuskarsa dukta d'auke, alamar ransa yana 6aci inhar ya tuna tushen ciwon. Cikin son kauda masa damuwarsa nayi murmushi ina d'ora hannuna mai lafiya saman nashi dake rik'e da mai ciwon, d'ago ido yay muka kalli juna, nad'an juya idanuna ina fad'in “yafi k'yau a haka ko?”. Hararata yayi kawai baice komaiba. Nayi k'aramar dariya. Yiyay tamkar zai matsa hannun nai azamar janyewa ina d'ane gadon gaba d'aya dayin y'ar k'arar tsorata, kad'an yarage na haye Amaturrahman. Murmushi yayi har hak'oransa na bayyana. yace, “ga tsoro ga tsiwa”. Nace, “naji dai ba komai”. Bai kuma cewa komaiba, sai murmusawa da yay, da kansa ya shafamin mai ya canjamin riga, dukda kakkauda fuskan kunya danaitayi, shikam ko a jikinsa, kai tsaye yake lamarinsa kuma hankali kwance. A gurguje please😏😜. ********************* Satina Uku a Asibitin aka sallameni, jikina kam sai godiyar ALLAH, dan na warke sarai, saidai y'ar ramar danayi, dakuma ciwon kai dake yawan addabata inhar waje yacika hayaniya. Tunda na dawo sai kuma kewar Galadima ta tasoni gaba, su Fauziyya nata shirin komawa gidajensu, sainaji inama harda mu🤭. Tunda na fito asibiti Aunty Salamah takuma k'aumi wajen bamu kulawa, musamman ma ni, dan ita Munubiya ina asibiti akaita mata nata. Tunda aka sallami Munaya daga asibiti ta koma gida sai yaji zaman k'asarma dukya gunduresa, ganin zai saka kansa a damuwa saiya had'a inasa-inasa yabar k'asar, itama Munaya rana tsaka yazo mata da zancen komawar. Addu'ar fatan alkairi kawai tamasa, da kuma sak'on magungunan Abie, a ranar yaso shiga su gaisa da baba mai kanwa, amma sai akaje wai bayanan, d'ansa yaje kaisa wani k'auye nan kusa gaisuwar Mutuwa da akayi. ............................★ Su momma sunyi farin cikin dawowarsa garesu cikin k'oshin lafiya, sai dai y'ar ramar da yayi. Shima wani matsanancin farin cikine ya kamashi ganin jikin Abie ya k'ara k'yau, yanzu har mitsa hanunsa yakeyi sosai, ga doguwar hira da akanyi dashi batareda ya k'osa ba, ranar sunsha hira sosai, har saida doctor d'in Abie yace subarshi ya huta sannan Galadima ya tafi gida shi da Momma, ranar Aunty Mimi aka bari wajen Abie tunda ita tasan komai. Sabuwar hira Momma da Galadima suka kuma dasawa a gida, dukkan abinda yafaru yabata labari dallah-dallah, dukda Aunty Mimi tabata dama, Momma harda hawayen jin dad'i, ta rungume Galadima tana saka masa albarka shida matarsa da yaransu. Babu kunya ya ringa amsawa cikin tsantsar farin ciki. Yanzu kam koba komai hankalinsa ya kwanta, ya maida hankalinsa ga dukkan aikinsa da sana'oinsa da suke samun kud'in shiga akan jiyyar mahaifinsa. Shiri yake a gaggauce saboda kiran da Doctor d'in Abie yamasa tun a daren jiya akan yanason ganinsa yau da sassafe. Yayi k'yau cikin Orange d'in Suit, sai k'amshinsa yake mai dad'i, cikeda salon birgewa yake sakkowa daga steps d'in benen yana waya, bayin daketa aikace-aikacen k'imtsa falon duk suka zube suna gaisheshi. Hannu kawai ya d'aga musu ya nufi hanyar fita a hanzarce yana cigaba da wayarsa, ya d'ora briefcase d'insa saman motar yasa key ya bud'e, bag d'in yafara ajiyewa gefen mai zaman banza sannan ya dawo ya bud'e ya shiga mazaunin driver ya tada motar ya fice. “Muftahu kabari zamuyi magana daga baya dai kawai”. Daga can Muftahu ya amsa da to babu damuwa. Ajiye wayar Galadima yay ya maida hankalinsa ga tuk'insa, yayinda sashen zuciyarsa ke tunano masa hirarsa da Munaya ta daren jiya, kwana biyunnan idan yamata maganar dawowarta saitai ta masa yawo da hankali, yarasa dad'inmi zaman can d'in yake mata? Ai wankan jegon ya isa haka, shima yana buk'atar zama da iyalansa koya samu nutsuwa tamkar kowanne magidanci, k'aramar tsaki yaja yana furzo isaka daga bakinsa, mata kenan, wataran su baka zuma, wataran su caja maka kai. Da wannan tunanin ya k'arasa asibitin, wayarsa kawai ya d'auka ya fita a motar, kai tsaye Office d'in Doctor Ajay ya nufa, yay Knocking aka bashi izinin shiga, (Abu Na CCTV suna kallon shige da ficin kowa) Doctor Ajay ya fad'ad'a murmushi sa yana mik'ewa, hannu suka bama juna cikin Musabaha suna gaisawa, Doctor ya nunama Galadima wajen zama. Bayan sun zauna Doctor daketa faman murmushi yace, “Sameer wani abun farin ciki ne nasamo a daren jiya, shiyyasa nakasa sukune saida Na kiraka a daren domin buk'atar ganinka”. Galadima dai kallonsa yake baice komaiba. Dr Ajay yaci gaba da fad'in, “Wato wani Doctor ne mai suna Dr Erfan Fahad Sajaad, d'an k'abilar Kashmir ne, Likita ne babban masani ta fannin irin matsalolin su Abie, yanzu haka yana k'asar England akan wani aiki, nakai watanni 6 inason ganinsa akan matsalar Abie amma ban samu damaba, saboda matuk'ar Busy dayake, sai a daren jiya nasamu magana dashi, bakaji farin cikin dana samu kaina a cikiba, dan mun tattauna sosai akan matsalar Abie, yanzu haka yabamu date d'in dazamu sameshi can Kashmir a asibitinsa”. Alhmdllh Galadima yaketa ambata a zuciyarsa tunda Dr Ajay yafara bayaninsa, cikeda farin ciki yace, “Doctor lallai nayi farin ciki da wannan albiahir naka sosai, ka wuce matsayin likita kawai a garemu saidai d'an uwa”. Murmushi Dr Ajay yayi, suka rungume juna shida Galadima kowa yanajin dad'i a ransa. Galadima ya fito d'auke da wannan farin ciki sukaci karo da Akash a hanya. Akash yace daddyn Triplets kenan, kwana biyu ka 6uya?. Hannu Galadima ya bashi yana fad'ad'a murmushinsa, yace, “Sorry my friend ka ganni dai yawo kamar ruwan sama, idan bani anan aganni acan, ya aikin?”. “Gashi munata fama, ya naka?”. Galadima yace, “Alhmdllh”. “Wai sai yaushe zaka dawo mana da Mummyn triplets ne? ga bikina yanata matsowa, bafa zan muku alfarma ba”. Murmushi Galadima yayi, ya dafa kafad'arsa yana fad'in “kwantar da hankalinka, ai babu yanda za'ai bikinka babu mu a wajen”. Aksha yace, “Ato kun wanke kanku, daga ina ka fito haka cikin farin ciki?”. Bayanin komai Galadima yayma Akash, dan baya 6oye masa komai gameda ciwon Abie. Shima ya nuna tsantsar farin cikinsa kuwa, kafin suyi sallama kowa ya nufi inda zaije. Waya yaciro yana lalubo number Munaya................✍🏻 *_Zan iya cewa yanzu zaku dinga rashin ganina, wlhy ammana haihuwar da tilas saina kasance a wajen a kullum, amma inhar Na samu time zaku dinga ganin posting, dan yauma banyi tunanin zanyiba, amma saigashi ALLAH yabani iko bayan dawowata daga asibiti, nima kaina Na k'agara nagama Na huta kuma Ku huta🤦🏻‍♀, I love you all😘😘😘😘❤🤝🏻_* *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [8/15, 6:54 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _____________________ *_ASSALAMU ALAIKUM_* _Tabbas da nayi niyyar ajiye RAINA KAMA saboda sakkayar da wasunku sukaimin, bazanyi ALLAH ya isa ga Wanda yafara fidda hotuna da nufin niceba, amma lallai koda ace aunty Ruk'ayya ce ko Ummi da muka fito ciki d'aya Na barsu da ALLAH, kai koda ace nina haifeta, ai kowacece ita ba dabba bace, kusan abinda ya dace da Wanda bai daceba, ba hotona nazo talla a social media ba, 😭kukuma masu gani da yad'awa jikinku Na rawa wlhy kushirya fidda hak'ina dake kanku a kotinda bakuda abin biyana sai ayyukanku, kunyi domin Ku tozartani saidai baku rageni da komaiba sai kanku, wannan abun yay matuk'ar 6atan rai fiye da zatonku, har yanzu idan Na tura raina Na 6aci, wlhy bazan zubar da hawayena a banzaba akan wannan abun, sai ALLAH ya fiddamin hak'ina akan kowacece ta fara turawa da masu cigaba da yad'awa😭, Ku miyasa Baku tura baku hotunanba? Da kunga Abu jikinku narawa kuhau yad'awa, saikace social media gidankune, ai cikinku babu Wanda baya banbance dai-dai da akasinsa, saboda kawai ina son nayi suna a gareku saina turo hotona nace kuyad'a, kwana nawama bana online d'in, inacan da damuwar son Na k'arasa muku abinda Na fara Ku kunan kuna cutar dani😭🤦🏻‍♀._ *Kosuwaye suje suda ALLAH, ALLAH kuma zai tozartasu suma fiye da Wanda suka aikata a gareni, Dan Na tabbata wlhy su ba masoyana bane, duk masoyina bazai aikata haka a gareniba,😭 kai ALLAH dai ya gaggauta sakamin kawai, bikin sallar da kowanne bawan ALLAH yake tsintar kansa a farinciki ammani kuka 6ata nawa da 6acin ran da bansan mafariba😭.* __________________________ *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣2⃣ .................Bata d'agaba dan haka ya maida wayarsa a aljihu yanufi d'akin da Abie yake jinya. ★★★★★★★★★ Zazza6in da innarmu ta tashi dashi yasaka mama Rabi'a zuwa dubata da iyalanta duka, kasantuwarmu waje d'aya a yau saiya bamu damar tuntu6ar sauran y'an uwanmu mizai hana mu tunkari iyayenmu da batin sanin asalinsu?. Damacan ya Marwan ne matsalarmu, danshi muke shakka, amma Alhmdllh Munubiya ta lalla6a manashi ya amince. Hasalima shine ya tunkaresu kai tsaye da maganar. Da farko shiru duk sukayi basu amsashiba. Saida ya Fadeel yace, “please iyayanmu Ku taimakemu Ku fiddamu daga wannan duhun, muma cike muke da shauk'in son sanin ina danginku suke, maybe hakan zai rage mana rad'ad'i da kewarsu, amma kuyi hak'uri idan mun Shiga hurumin daba namuba”. Innarmu ta sauke ajiyar zuya daga kwancen datake, ta kalli Mama Rabi'a datai k'asa dakai idonta cike da kwalla, tashi innarmu tayi zaune tana kallonmu d'aya bayan d'aya, ganin duk mun zuba musu idanu saita murmusa, cikin dakiya tace, “Nasan wannan tambayar ta dad'e tana cinku tsawon shekaru, dukda nuna mana da kuke Na buk'atar sanin su wanene mu amma muna sharewa, ina mai muku albishir da lallai wannan karon zaku samu dukkan amsoshinku daga garemu, amma ta hanya guda d'aya tak”. Kallon juna muka shigayi, kowa yana mamakin wace hanyace wannan?. Murmushi innarmu ta sakeyi, tana fad'in “karku zurfafa tunani, hanyar dai bata wuce shirya tafiya gaba d'ayanmu domin waiwayar ahalinmu ba, duk da kuwa su basa buk'atarmu a cikinsu, saboda kasantuwarmu jinsin da basa baraba dashi a tsarinsu, jinsin da basu shirya kar6aba saboda wani al'adar banza mara amfani da amfanarwa, sun mata dukkan saurinsu sai sunjira ALLAH. Munaya yanzu kece kad'ai matsalarmu, saboda bamusan ko mijinki zai aminceba, amma ki tambayesa, inhar ya amince to lallai k'arshen satin sama zamu tafi”. Gaba d'ayanmu farincikine ya baibayemu, kowa fuskarsa a washe, ya Marwan sarkin miskilanci ne kawai yay d'an murmushi, amma fuskarsa shima ta nuna alamar jin dad'in hakan. Farin cikin damuke ciki yasani bamma San Galadima ya kiraniba, saida Na d'auki wayar da nufin kiransa na fad'a masan zancen tafiyarmu ne sannan naga kiran, idanu Na waro waje, Na mik'e ina barin cikinsu Ayusher danma karsu isheni da hayaniya. Harta tsinke bai d'agaminba, nakuma kira nanma baiyi picking ba, sainaji duk babu dad'i, kardai fushi yayi?, k'ok'arin rubuta masa massege Na fara saiga kiransa ya shigo. 'Dagawa nayi da sauke ajiyar zuciya, Galadima dake zaune bakin gado sanye da bathrobe Dan yana wanka taita kira. Murmushi yayi mai sauti har tana jiyoshi, cikin sanyin Murya yace, “wannan ajiyar zuciyarfa?”. Tsayuwa Munaya ta gyara, da y'ar shagwa6a tace, “Ba kaineba”. “Tofa, ni jikan Abubakar da Abdul-fatah, ni minayi kuma?”. “Shine naketa kira kak'i d'agawa”. “O, Na ramane nima. d'azun ban kiraki ba? Amma baki d'agaba, bakuma ki biyoniba, awa nawa kenan?”. “Kayi hak'uri My king, wlhy ban kulaba sai yanzu, hirace ta d'auke hankalina, Su Ayusher duk sunzo duba Innarmu”. “Humm, toya jikin inna?”. “Alhmdllh ai tama warware, yasu Momma da jikin Abie”. “Everything Alhmddllh, ina maganarmu ta tsaya?”. Dafe kai Munaya tayi, ta zauna saman katifar su Aryaan, tawani narke murya da shagwa6eta, “Haba yalla6ai miyasa kakeda son maida zance bayane? Ba mungama da wannaba?”. 'Dan kausasa muryarsa yayi. Yace, “Munaaya! Nagaji da wannan yawo da hankalin, shin wai k kam bakida tausayine? Nifa ba dutse bane, ko har yanzu baki yafemin kuskurena bane ba?”. “Kayi hak'uri to, dama yanzu wata mafita Na samo, dan wlhy kunya nakeji, bazan iya tunkarar inna nace mata zan komo ba”. Kamar bazaiyi maganaba, harma Munaya ta fidda tsammani saikuma taji muryarsa a sanyaye yace, “Miye mafitar?”. Kwanciya munaya ta gyara jin tafara samo Kansa, Dan burinta kawai ya amince suyi tafiyar, sauran zance saita dawo sayi. tace, “Yauwa Autan Momma bud'e kunnenka da k'yau kasha labari”. Murmusawa yay kawai yana zamewa ya kwanta shima, wayonta Na birgeshi, inhar zai 6ata rai akan Abu tasan hanyar da zatabi ta bashi nutsuwa. yace, “ina jinki”. A nutse tabashi labarin zuwansu Niger domin ganin danginsu inna, a salon data fahimtar da shid'in lallai ya fahimta, saidai amsa zai barta zuwane yad'anso yin gardama, saida ta kalallameshi da dad'in baki da magiya sannan ya amince akan shima zai biyo bayansu, daga nan zai d'akkota su taho. Kai tsaye tace ta amince. Yayi farin cikin da hakan, yabata labarin shima yanda sukayi da Dr Ajay. Yanda ta nuna tsantsar farin cikinta da murna akan lamarinne Yakuma saka masa nutsuwa akanta, soyayyar da takema mahaifansa da dukkan ahalinsa shine makamin farko data fara amfani dashi wajen bige dukkan yak'ininsa akan shirin Auren contract, takuma k'ara kima da daraja a idonsa. Daganan suka cigaba da hirarsu ta soyayya anutse, abin akwai birgewa. Yace saita sakashi yayi barci sannan zata kashe, wannan ne punishment d'inta. Babu yanda ta iya dole ta bishi yanda yakeso, har saida taji tsitt alamar yay barcin da gaske sannan ta kashe tana dariyar wannan shagwa6a ta Galadima, a yanzu Idan yamata wani abun takanyi mamakin dama haka yake?. Aiko data koma d'aki tasha tsiya wajensu Feena, sai banza tamusu sukayi mai isarsu. ************************ Kamar yanda shirye-shiryen tafiyarsu Munaya Niger ta kankama haka shirin kai Abie Kashmir wajen Doctor Erfan Fahad Sajaad ta kankama suma. Y'an gidansu Munaya dai ansamu abinyi, sai gulmace-gulmace da gugar zana sukeyi akan wannan tafiya, harda masu fad'in talauci da wahalane ya koro su inna, yanzu anga ansamu arzik'i za'a koma k'auye amusu iyayi da farfaganda. Duk abinda ke faruwa Inna naji kuma tana saurare, amma baiwar ALLAH sai dai tayi Murmushi kawai, takuma hana su Munaya cewa komai, har Innaro saida ta yaddama Inna habaici akan wannan tafiya. Su Maman ya Hameed akaita dariyar gatsatsa. Wannan abin da inna taga sunayi ya sakata rok'on Abba akan tafiyarnan yakamata ace Innaro ma aje da ita. Abba bai kawo komai a ransa ba ya amince, harma ya nuna mata farin cikinsa, yakuma shiga yima Innaro shiri itama __________________________ Dukkan shirin da ake buk'ata nakai Abie Kashmir ya mammala, Galadima da doctor Ajay da Dr Akash ne kawai zasuje, Anbar su Momma gida su huta, duk da taso binsu amma Galadima ya lalla6a ta dai ta zauna. Ta jirgi suka tafi, dukda bawani insane mai yawaba, to amma jikin Abie bayason yawan matsala da takurar zafi. Suna Isa Ambulance tazo ta d'aukesu. Asibitin bawani k'ato baneba, hasalima Wanda Abba ke ciki a new Delhi yafi wannan girma da k'ayatuwa, dukda shima wannan d'in ya had'u bakin gwargwado, sunkai 3hours zaune basu sami ganin doctor Erfan ba, dukda kuwa shine yabasu wannan date d'in domin ganinsa, andai shiga da Abie wani d'aki tun zuwansu. Ran Galadima ya fara 6aci, abinka da ba sabawa yay da hakan ba, zai fara k'orafi saiga doctor Erfan Fahad ya fito daga wani d'aki, da alama ma wani aikin yayi a ciki, su Galadima basuga fuskarsa ba harya shige Inda suke tunanin Office d'insane. Wajen 30minute's da shigarsa sannan aka basu izinin shiga. Sai wani cika da batsewa Galadima yakeyi Na haushi, shi dai Dr Ajay yanata lallashinsa akan inhar zasu sami biyan buk'ata ai hakan ba komai baneba. K'ala dai Galadima bai ceba. Doctor Erfan Fahad Sajaad, matashin likita dabazai wuce sa'ar Galadima ba, k'yak'yk'yawan ba indiye mai tashe da lokacinsa, Wanda duniyace ke amfanuwa da fik'irarsa bawai India ko yankin Kashmir kawaiba. Kallo d'aya Galadima yamasa ya d'auke kansa, Dr Erfan ya ajiye file d'in Abie dayake dubawa yana fad'in “Kuyi hak'uri dani Brother's, aikine babba ya dinkareni daga cika alk'awarin Dana muku, gashi kuma Na gaggawa”. Galadima ya juyo da nufin juye masa abinda ke ransa sai kawai doctor Erfan Fahad yad'anyi baya cikin mamaki. Yace, “Waishi wama nake gani a gabana kamar Muhammad Sameer Saifuddin?”. Galadima da mamaki ya kasheshi yace, “lallai shine, amma a ina kaimin wannan sanin haka?”. Wata dariya Dr Erfan Fahad yayi, yad'an bigi tebir d'in gabansa yana fad'in “Duniya labari, Muhammad Sameer Saifuddin kenan! Nikam kaga koda saida muka tsufa Na ganka saina ganeka wlhy, shin zaka iya tuna wani Wanda kukai karatun Addini shekaru 19 da suka shige a wajen Sheaik Mu'azzam Abdul'aziz khan?”. Shiru Galadima yay ya lula duniyar tunani, Dan a yanzu yad'an fara d'ago fuskar Dr Erfan Fahad d'in. Dr Erfan Fahad ya d'an daki kafad'arsa cikin dariya, “My friend mu ajiye wannan chapter d'in, tana buk'atar nata time d'in, amma lallai nayi farincikin ganinka bayan tsawon shekaru Dana d'auka wajen nemanka, kardai kacemin har yanzu Abie yana jinya?”. Ajiyar Zuciya Galadima ya sauke yana jinjina kai, danshikam tunanine dank'are a ransa gameda Dr Erfan Fahad Sajaad d'in. Dr Erfan Fahad yace, “Abie ne mutum Na farko daya fara fad'omin a rai bayan zamana cikakken likita kwararre ta fannin irin matsalarsa, sai dai duk tunanina shi yasamu lafiya, Ashe yanata ibadar ALLAH har yanzu, insha ALLAH matsalarsa tazo k'arshe kuwa, Doctor Ajay nadawo gareka, ina buk'atar k'arin bayani gameda magunguna da Abie yakesha?”. Dalla-dalla Dr Ajay ya shiga ma Dr Erfan Fahad bayani, Galadima dai Na saurarensu, dukda Rabin hankalinsa naga son tunano wanene Dr Erfan Fahad?. Bayan Dr Erfan Fahad yagama sauraren Dr Ajay, shima yaymusu bayani dalla-dalla akan alurai daza'a dungama Abie duk bayan wasu awanni. Allurarce zata zama makarin wannan ruwan guba daya gauraye dukkan jijiyoyinsa, ahankali zasu fara motsawa daga dakatar dasu aikin da akayi da wancan poison d'in, daga nan ga66an jikinsa saisu fara aiki insha ALLAH. Dukda nauyin tsadar wannan Allurai haka Galadima ya amsa, yasan tattalin arzik'insa ba k'aramar girgiza zaiyiba, Dan harma saiya had'a da saida wasu kadarori, bashida burin dayafi yaga Abie yasamu lafiya, koda ace dukkan dukiyarsa zata salwanta bazaiyi bak'in cikiba, fatanshima ALLAH yabashi ikon had'a dukkan kud'ad'en da ake buk'atar batareda ya dogara da taimakon kowaba. Masauki Na musamman Dr Erfan Fahad yabama su Galadima, dukda Akash yashiga gari ya sama musu, amma Dr Erfan Fahad yace Sam bazai yuwuba, a gidansa zasu sauka tilas. Bayan sun sami nutsuwa, Galadima yayi wanka ya kira Momma yamata bayani akan komai, hankalinta ya tashi kwarai da gaske, Dan kud'ine masu yawa, wad'anda tana k'yautata zaton dawuya ace Galadima yanadasu gaba d'aya. Amma jarumin naku saiya shiga kwantar mata da hankali akan Neman nasara da addu'arta. Fatan alkairi taita masa da fatan dacewa. Yana yanke wayar ya kira Baffi suka tattauna shima akan kaddarorinsa daya kamata a saida, danshima dai shine lauyan nasa. Sosai Baffi ya tausaya masa, Inda ace shid'in wanine tabbas daya taimakama Galadima da iya k'arfinsa, amma ina, a abinda ake buk'ata shiba komai baneba, Dan ko kud'in ruwan allura d'aya ba iya saya masa zaiyiba. Haka ya shiga shigi da fici akan dukkan abinda ya dace. A nanma Galadima ba zama yayba, washe gari yabaro Kashmir shida Akash suka dawo India, Dr Ajay kawai suka baro can, wasu kud'ad'en ya fara turawa dake hannunsa, Dr Erfan Fahad yafara treatment d'in Abie. ************************** Busy da Galadima yayi yasaka shi da Munaya waya sai time to time sukeyinta, a koda yaushe kuma cikin kwantar masa da hankali take, a Daren da zasu wuce Niger nema suka d'anyi doguwar hira, yayta shinfid'a mata dokoki akan yaransa, ita dariyama abin yayta bata, ta dai danne da binsa da to Dan a zauna lafiya, ta d'ira da masa godiyar hidimar da yasaka Muftahu ya kawo musu da sunan tsaraba da dukkan abinda zasu buk'ata, wai ba sai sunje sunkaima mutane nauyiba. Washe gari suka Nufi Niger Republic cike da zumud'in son kasancewa da ahalin mahaifansu. Tafiyace da sukayi cikin isassun motoci babu takura, Dan Galadima motoci ya aiko musu har hud'u, wad'anda zasu iya jurar dukkan wata wahalar shiga sahara, tareda kwararrun driver's da sukasan hanya. gashi basuda matsalar Abinci dan sun tanadi abinsu. Tafiyar sassafe sukayi. Dukda sakko da sukayi basu sami shiga Agadas ba a ranar, dole suka sami mafaka suka kwana, ranardai kam babu maganar waya da kowa dake Nigeria, balle kuma su Galadima. Sosai Munaya taji kewar mijinta, balle da taga su Munubiya nata soyewarsu, hasalima d'aki d'aya suka sauka a masaukin, itakam itada laraba saboda kula da yara. Ya Marwan kam shi ai gaba ta kaishi, dan wannan damar ya samu ya more amarcinsa, Dama an dad'e ba'a had'uba🤭. Dukda magiyar da Munubiya taita masa akan yabari saisun koma gida amma yace Sam bama ta isaba, yaudai saiya lasa, dole ta barshi yayi yanda yakeso harma da bashi gudunmawa, dan sunyi missing juna, saidaga baya taita masa zun6ure-zun6uren baki, shikam yayata mata tsiya da gwalo. Da safe Munaya yanayinta kawai ta kalla taita shek'a dariyar mugunta, harda Munubiya ta tsargu. Su Feena nata tambayar Miye?. Munaya tace, “kuma Ku gano da kanku, dan babu ruwana”. Su Ayusher dai basu fahimci komaiba, har Munaya tagama shak'iyancinta tayi shiru a motar. Yau d'inma dai sai yammaci lik'is suka isa Cikin Birnin Agadaz. Dan anata kiraye-kirayen sallar Magrib. Tunda suka shigo garin inna tai zugum tana tuna wasu shud'ad'd'un shekaru da abubuwa masu yawa suka faru, babu inda tagane saboda dad'ewar da sukai da barin tushensu, garama ita, mama Rabi'a ma bata fahimci komaiba ita, dan wayonta a wancan lokacin baikai Na inna ba. Kula da damuwar da inna take cikine ya sama Abba kama hannunta ya rumtse a nashi alamar lallashi. Batace dashi komaiba, sai d'ora kanta datai gefen kafad'arsa. Driver dake driving motar dasu innar suke ciki yace, “Hajiya ina muka dosa to?”. Shiru Inna tayi takasa magana, saboda kuka daya taho mata, tana fargabar ko zasu sami k'ar6a daga ahalin nasu kokuwa sa6ananin hakan, gashi harda uwar gayya sukayo. Mama Rabi'a ce tai k'arfin halin cewa “Zamuje masarautar garinne”. Daga Abba har Abbansu Feena kallonta sukayi da matuk'ar mamaki, mama Rabi'a dai tai k'asa da kanta, dan batada bakin amsa musu dukkan tuhumarsu. Inna kam ai saita fashe da kuka k'asa-k'asa. To Mudai bamusan ina aka dosaba, kallon gari kawaine namu, ni inata fama da Abdurraheem ma dake kukan gajiya, nasan wanka kawai suke buk'ata, shine zaimin bore, ALLAH ma ya soni Sauran basu d'auki amshiba, dan duk suna hannun su Feena da muke tare a motar. Innaro dai tanata baza ido da ta6e baki, burinta dai a Isa taga abinda yasa aka tasosu daga wata uwa duniya. 🤣innaronmu ta mutunci badai za'a canjaba kam.🤦🏻‍♀ Duhun da dare ya farane yasa bamu fahimci inda muka iso ba, inna tasan baza'a ta6a barinsu shiga masarautarba kai tsaye, Dan haka ta fita daga motar, takai mintuna kusan 20 tana fama da masu tsaron k'ofar, amma sunk'i aminta da shigarsu, dukda kamaninta da suke hangowa dana ahalin masarautar. Ana cikin haka saiga wani matashin saurayi dabazai wuce sa'ansu Yaa Marwan ba. Yanda yake tafiya cikin tsari da Isa zai tabbatar maka shi jinin gidanne, masu tsaron k'ofar duk suka zube k'asa suna masa barka da fitowa, bai amsa musuba sai inna da yaketa faman bi da kallo, itama dai idonta na'a kansa. Kamannin mahaifinta take kallo tsaf tattare da saurayin, yayinda shima dai take masa tsananin kama da nasa ahalin, ya d'auke kai da nufin barin wajen batareda ya tankama innarba, murmushi tayi kawai, Dan shariya da Isar mulki wannan jinin gidansune, shiyyasa mafi yawan lokaci ba hak'urine kawai ke sakata share haukar y'an gidansuba, harda wannan halayyar data zama jinin jiki. Cikin harshen buzanci tamasa magana. Cak ya tsaya, kusan wasu seconds sai kuma ya juyo yana kallonta. Inna tace, “dukda banida hurumin tambayarka wanene kai a masarautar nan, domin yanayinka ya tabbatar min kasancewarka jinin gidan, ina rok'onka alfarmar tambaya da kuma taimako”. Nanma kallonta kawai yake, tamkar bazaiyi maganaba saikuma ya matso gabanta, alamar yana saurarenta. Sunayen mutum uku ta lissafo masa akan ko sunada rai. Da mamaki sosai yake kallonta, dukda yanayinta ya nuna ita buzuwace, amma ba mazauniyar wannan yankinba, Dan suturarta da wasu abubuwa da dama ya banbantata al'ummar yankin, gashi kuma ta lissafa masa sunayen manyan mutane masu daraja a masarautar. Shima cikin harshen buzancin hace, “baiwar ALLAH ked'in wacece?”. “ta hanyar shiga damu wannan gidan kawai zakasan wacece ni”. 'Dan jim yay alamar tunani, zuwa can sai yace, “ina zuwa to”. Kai inna ta jinjina masa, ya koma ciki, inna kuma tadawo jikin motarsu tana bama su Abba hak'uri. Sukace karta damu, tabi ahankali. Kusan mintuna 30 saiga saurayinnan ya dawo tare da wasu tsoffi biyu, inna Na hangosu ta nufosu itama, bata ganesuba, amma haka ta risina tana gaishesu cikin yarensu. 'Daya a cikinsu tamata wasu y'an tambayoyi, duk inna ta amsa mata kai tsaye, mamaki ya kamata, takuma jeho mata wata tambayar, nanma dai inna ta amsa. Tsohuwa tayi murmushi, sannan tabama masu tsaron k'ofar umarnin barin motocin su inna shiga cikin masarautar. Inna taji dad'i sosai, taita mata godiya. Shigarmu katafaren gidan mai yalwace da haske a ko inane yabamu mamaki, bayan driver's d'in sun faka motocin inda aka nuna musu duk muka fito, mudai kallon kallo muka koma a tsakaninmu, Dan munga abinda ya girmi tunaninmu, hadimai sai kai kawo sukeyi dukda duhun dare. Iya abinda zamu iya buk'ata kawai aka fidda mana a motocinmu, tsaffinan da matashin saurayi daya maidamu television sukai mana iso wani Sashe, babu kowa amma cike yake da komai Na buk'atar rayuwa, yayinda kwanmu da kwarkwatarmu zai ishemu mu sakata mu wala. Mun gaida tsoffi nan dukda bamu da tabbacin sun iya Hausa, amma a mamakinmu duk sai suka amsa mana, suka kuma mana sannu da zuwa sannan suka fita, amma banda wannan saurayi daya koma gefe ya zubama dukkan wani motsinmu ido, musamman ma mu hud'unnan, Ni munubiya Ayusher Feena, bansan miyake kallo tattare damuba, nidai damun had'a ido dashi saina zuba masa harara, yakanyi murmushi ya d'auke kai, Ashe sauran y'an uwanama hakance ke faruwa a tsakaninsu dashi. Yaa Marwan da Fadeel kuma suna lura daduk abinda ke faruwa, amma suka k'i cewa uffan. Dan yak'ima kowa magana a cikin mu, shiyyasa muma duk mukayi watsi da lamarinsa, babu Wanda ya tanka masa. Babu jimawa saiga tsoffi nan sun dawo tare da wasu y'ammata kusan goma, kowacce abinda ke hannunta ta ajiye, sannan duk suka durk'usa suna gaishemu. Tsoffi suka sake zama muka gaisa, sannan suka nunamana d'akunan barci, dacewar mu huta zuwa safiya koma mikenan dai saji. Innaro dai bin kowa take da ido, ga gajiya Na cinta ga tambaya fal ranta, dasun had'a ido da inna saita sakar mata murmushi kawai, hakama Abba da abbansu Ayusher, saibin matan nasu suke da kallon tuhuma, amma su inna sunk'i bada dukkan k'ofar da kowa zai fahimci wani Abu. Saurayinan ya fice bai tankama kowaba, yana fita muka shiga ta6e baki. Amma bamuce uffanba dai. Nace, “Ni dai bata abincinnan nakeba, nasami ruwa nayi wanka shine matsalata”. Hararata mama Rabi'a tayi, tana fad'in “Baki da tausayi Munaya, wad'annan bayin ALLAHn ai suke buk'atar duk wannan bakeba, musamman Abdurraheem dashi baima son takura Na kula”. “Yo mama nidai kaina Na sani wlhy”. Rankwashi Yaa Fadeel ya zubamin akai, Na dafe wajen idona Na cikowa da kwalla, “Amma Yaa Fadeel da zafifa?”. “Ai dankiji zafin namiki”. Yanda nahau matsar kwalla duk sai suka haumin dariya, hardasu Abba, haushin hakan yasani tashi Na shige d'akin dake kusa da inda muke zaune. Kutt d'akine k'ato, d'auke da makeken wani irin gado mai k'yau, saida nayi bismilla sannan Na fad'a saman gadon, Dan tsayawa muku lissafin had'uwar d'akin 6ata lokacine, ahaka Ayusher ta shigo ta sameni, muka 6ararraje abinmu. *Bayan awa 3* Duk d'inmu kowa yayi wanka ya canja kayan barci, yaranma an musu, munci abincin dai sama-sama, Dan ba irin cimar da muka saba baceba, amma dayake akwai fruits dawasu abubuwan irin shigen abincinmu sai muka harhad'a mukai nak, garin dad'an sanyi gaskiya, aka nad'e su Ameen cikin kayan sanyi su duka, kowa d'akin da yay wanka yakoma ya kwanta a matsayin masauki. Mudai tare da innaro da laraba muka kwana, saboda matsalar yara. To dayakema kowa gajiya taci k'aniyarsa lafiyar ALLAH mukasha barcinmu, amma wlhy akwai d'an karen sanyi, Dan zuwa asubahi harda wata iska mai azabar sanyi daban tsoro, ALLAH ma yasomu akwai manyan barguna a d'akunan, gakuma ko ina ruf an d'auki mataki, da alama sun saba da kayansu su dama. Tunda safe sosai aka kawo mana karin kumallo a kuloli masu k'yau. Mudai kam bama mu tashiba, saisu innarmu, koda hadiman dazasu mana gyaran sashe. Sukazo sai komawa sukayi, dan barci muke, su Abba ne kawai suka tashi dasu innarmu. Kusan awanni biyu da kawo abincin tsoffi nan sukazo kiran inna, sai suka tafi da mama Rabi'a, mu munatama barcinmu bamusan duk anayiba. Tunda suka fito idon Inna ya cika da hawaye, yau sune a mahaifarsu, bayan tsawon shekaru da suka d'auka basannan, sosai masarautar ta canja, an k'awatata fiye da da, abubuwan cigaba masu d'unbin yawa sun yalwatu a cikinta, ga gine-gine Na k'awa da akayiyyi cikin masarautar. Itama dai mama Rabi'a bata tuno komai dan sanda sukabar masarautar bama tasan kantaba. Sun isa wani Sashe mai girman gaske da k'awa, kamar yanda kowanne bango yake da hoton Rak'umi haka shima wannan, an k'awatashi da hoton rak'uma har Uku, hadimai sai mik'a gaisuwa suke gasu inna, nasudai d'aga hannu da murmushi, Dan ita inna ta mance abubuwan da yawa da suka shafi tsarin masarautar tasu, to bama wayaune da itaba awancan lokacin, sai y'an abubuwan daba'a rasaba. Sun Isa katafaren falon daya k'awatu da kayan alatu irin Na yankin nasu, basu tsaya ananba sai a wani dake gabansa. Buzuwar tsohuwa ce k'yak'yk'yawa, mai cike da d'umbin kamala da halin dattako, tana zaune bisa wata darduma ruwan goro, hadimai biyu namata hidima. Batako d'ago kai ta kalli kowaba, dukda tasan da shigowar su inna, Tsoffi nan guda biyu suka rissina suna sanar mata zuwan su inna. Mayafin dake yane da jikinta Na yadin lafaya irin kayan buzaye ta janye saboda rufe mata rabin fuska da tayi, ta d'ago kai tana kallonsu inna Wanda suma itad'in suke kallo. Wani Murmushi ta sakar musu Na musamman, yayinda idonta ke binsu da kallon k'urilla mai nuna alamun kallon kamannin wani a jikinsu. Cikin yarensu Na buzaye tama tsoffin da hadiman Umarnin ficewa. Saida suka fita sannan ta yafito su inna alamun su matso gareta. Inna da mama Rabi'a suka matsa inda take, ta kamo hannayensu ta rik'e a nata tana murzawa, kusan mintuna biyu, sudai su inna Na kallonta, tamusu nuni da subata tafin k'afarsu ma. Inna a ranta tana mamakin kenan har yanzu canfe-canfe da muguwar al'adar gidan Na nan dai?..... Tunaninta ya katse lokacin dataji hannun tsohuwarnan bisa fukarta, kallon juna sukayi itada mama Rabi'a, sannan suka maida kallonsu ga tsohuwar da idonta ke a rufe tana murmushi da cigaba da shafa fuskokinsu. Kusan mintuna biyu sannan ta bud'e ido akansu, race, “lallai kud'in ahalin wannan gidane Na gaskiya, masu tafe da babban abin al'ajab da ba'a ta6a samuba a wannan masarautar, barkabku da dawowa hamshak'iyar masarauta mai d'unbin tarihi da yalwar arzik'i, minene sunayenku?”. Cikin had'iye yawu inna tace, “Ni Ai'sha, itakuma Rabi'a ”. Tsohuwa tayi murmushi mai k'ayatarwa, sannan tajawo kaskon wuta dake cike da rushi gabanta, ta bud'e wani kasko mai k'yau ta zuba garwashi kusan bakwai sannan ta saka turare mai d'unbin yawa a ciki, dandanan wani k'amshi ya baibaye falon, gabansu inna ta tura kaskon, ta jawo wani mayafi ta mik'a musu da musu nuni su rufa dashi. Basuyi musuba, Dan ita inna duktasan hakan al'adar masarautar suce. Haka suka shige mayafin k'amshin yanata baibayesu, kusan mintuna biyar ta bud'esu da kanta. Babu Wanda yay magana tsakanin ita da su, saiga mutane sun fara shigowa d'ai-d'ai cikin falon. Kowacce cikin shiga ta alfarma irinta cikakkun Buzaye, hakama mazan, kowanne fuska a nad'e cikin rawani. Dukkan mai ruwa da tsaki saida yagama hallara, adadin wasu mintuna saikuma ga wani dattijo mai cike da tarin kamala ya fito ta wata k'ofa daban, a tare dashi da mata biyu suma cikin nutsuwa, kowa saida ya mik'e a falon har wannan tsohuwa. Dattijo ya zauna bisa kujera dake gefe, sannan kowama ya zauna, cikin risinawa sukaita gaisheshi, kansa kawai yake jinjina musu, hakanne yasakasu inna fahimtar lallai wannan shine Sarki mai mulki a wannan masarauta yanzu. A cikin nutsuwa yay magana, idonsa nakan mama Rabi'a da inna. “Lale marhabun da dawowarku wannan masarautar mai d'unbin tarihi da dattako, mai takaici dakuma dana sanin farrak'a mafi yawan ahalinta bisaga bahaguwar al'ada mai durk'usar da kowanne irin ahali”. Idon Inna cike da kwalla, da d'okantuwa da furucin wannan adalin Sarki mai kama da jirwayen nadamar kasatuwar abinda ya wanzu abaya dama Wanda basuda tabbacin faruwarsa ko dakatawarsa. “Muna godiya mai cike da girmamawa da farin cikin waiwayen bayanmu dukda muna tare da fargabar koza'a kar6emu, amma lallai an ciremu daga wannan fargabar da muka shigo da ita wannan yanki”. Dattijo ya jinjina kansa yana murmushi. Tsohuwar d'azunce ta kalli dattijon Sarki, ta buk'aci shigowar sauran tawagar bak'in dasu inna sukazo dasu. Kai tsaye yabada izini. Kwammu da kwarkwatarmu muka shigo, hardasu Aiyaan dasu Innaro, duk muna d'auke dasu Amaturrahman, nanma dai abin kallon muka gani da mamaki, tamkar yanda muka baro wasu abaya, mun kasa fahimtar inane su Innarmu suka kawomu kuma?. Gaisuwa mukaiyi irin wadda muka iya, hakama su Abbanmu da aka bama wajen zama Na musamman a gefen wannan dattijo. Duk sun kar6a mana a yanayin kallo da son sanin su waye mu?. Irin turaren da akaima su inna suma su Munaya saida aka musu, dukda su ba'a rufesuba, aiko su Meenal sukaita atishawa, mudai harma muka tsargu. Tsohuwar nan daice ta mik'e tana Neman sanin daga ina muke? Su waye kuma su inna?. Inna ta mik'e tsaye, cike da girmamawa ta maimaita musu sunanta, sannan tafara koro bayani kamar haka..................✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [8/15, 6:54 PM] 0mmer Farouk: [8/9, 5:40 PM] 🙇🏻‍♀Da Rarrafe🙇🏻‍♀: [8/9, 12:53 PM] 🙇🏻‍♀Da Rarrafe🙇🏻‍♀: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣3⃣ .................Mud'in mun kasance wasu yankin ahali daga wannan masarauta, sai dai nasan al'ada da ak'idar masarautar ta jima da shafemu daga kasantuwar tsatsonta. Iftila'in al'ada Nak'in kar6ar d'iya mace a matsayin y'ar farko ga Sarki mai mulki shine silar barin iyayenmu damu kanmu, sarakuna da yawa sun shud'e labarinsu ya shafe tamkar yanda Na Sarki Madou Amadi yazama shud'ad'd'e” inna ta share hawayenta, sannan tacigaba da fad'in, “Lokacin da mahaifinmu yake bisa karagar Mulki da k'arfin iko sai ALLAH ya azurtashi da haihuwa ta a matsayin d'iyarsa ta fari. Haihuwata ta girgiza k'arfin mulkinsa matuk'a, Dan Al'adar masarautar shine tilas d'an Sarki Na farko ya kasance d'a namiji, acewarsu d'iya mace rusa masarauta takeyi da tsiyatata, dan ita bata mulki, kamar yanda ake korar duk wani Sarki da matarsa ta haifi y'a mace a haihuwar farko ga mahaifinmu sai bai yuwuba, saboda k'arfin iko da ALLAH ya bashi, anbuga-anbuga yak'i sauka, danshi burinsa ya canja wannan al'adar masarautar, har ALLAH yasa Na cika shekaru 7 a duniya. A tsakaninnan bayyana harmutsi da hayaniyar da taita faruwa 6ata lokacine, Dan mahaifinmu Sam yak'i sauka daga Matsin da suke masa. cikin amincin ALLAH sai kuma ga cikin Rabi'a babu zato, har wannan lokacin babu wani kwanciyar hankali a masarauta, saidai bayyanuwar cikinta yasa akace za'a dakata aga mizata haifa, idan d'a namijine shikenan. Saidai kash, daga lokacinda Rabi'a ta canyara kukan isowa duniya sai masarauta tayi tsitt, Dan kuwa dai kowa yaji macece. Dandanan fa aka tada Sabin bore akan dolenefa sarki ya ajiye a wannan karon, amma mahaifinmu saiya k'i a wannan karonma, danshi burinsa ya canja wannan mummunar al'adar kowa ya fahimci itama d'iya mace tanada tata darajar fa, kufa namijin bai fitaba, domin itama ALLAH ya haliccetane danta bauta masa tamkar namijin, dukansu kuma idan sunk'ibin ALLAH wuta zai sasu, idan sun bishi Aljanna zai kaisu, amma Sam sai suka bijirema dukkan tunatarwarsa, masuma goya masa baya suma sai suka daina, watan Rabi'a 1 kacal a duniya akai mana korar kare daga wannan masarauta dama yankin baki d'ayansa, muna kuka muda mahaifinmu haka muka tafi, mukabar ahalinmu, yankinmu , al'ummarmu. Saboda mummunanr Ak'ida, saidai kuma babu inda muka Sani, Dan haka iyayenmu suka yada zango awani k'aramin k'auye dagacan bakin gari, anan muka rayu tsawon wasu shekaru dahar nakai girman zama minzalin budurwa, itama Rabi'a ta girma, rana tsaka saiga tawagar masarauta wai ankai mata bayanin mahaifinmu baibar wannan yankiba, halan akwai abinda yake shiryawa? Dan bazai yuwu ayi sarki biyu cikin nahiya d'aya ba, sarkin ma da aka d'ora bayan korarmu shima matarsa mace ta haifa, tuni sun korashi, Na yanzunma kuma hakance ta faru, dalilin korarsane ma sukaji labarin mahaifinmu yana a wannan waje tare damu. Korar cin zarafi da akai mana a wannan lokacin tamafi Na farko, Dan alokacin munada wayo muma, munsan zafi munsan d'aci, a wannan karon bama Nahiyarmu ba, k'asar gaba d'aya muka bari, tafiya ta tsawon wattani da yada zango ce takaimu Nigeria, a wahalce a jigace, inda muka samu mafaka a tashar da suke lodin motocin da suke zuwa kasuwanni, makonmu uku a wajen, Dan bamu rasa abincin dazamu ciba iftila'in rayuwa da k'addara ta fad'amin, Wanda muka wayi gari da rashin mai taimakonmu sai wani bawan ALLAH (Malam fharuku kakansu Munaya😅)” Inna taci gaba da bada labarin k'yautatawar dasu Innaro sukai musu, har mutuwar iyayensu da aurenta da Abba, Dana mama Rabi'a, da zuri'ar da suka samu harda jikoki, ko kad'an bata fad'i muzanwa ko cin fuska da Innaro taita musuba sai alkairin mijinta da y'ay'anta. Nanfa kowa ya shiga matse hawayen tausaya musu, hardamu, Dan munji abinda koda wasa bamu ta6a saniba balle tunanin kasantuwarsa, Dama iyayenmu jinin sarautane mai girma irin haka? Amma kullum suka kasance cikin shanye k'ask'anci da gorin talauci Dana ahali, lallai wannan banzar al'ada batada wani abin birgewa. Shikansa sarkin saidai yay hawayen tausayinsu inna, Yakuma buk'aci su matso garesa, hakama tsohuwarnan rungumesu tayi tana kuka. Innaro dai anyi zugudim tana kallon ikon ALLAH, Wanda ya girma ya d'aukaka, kunya da d'unbin nadamar Dana Sani sun dabaibayeta tagaza koda kwakwkwaran motsi balle d'aga ido ta kalli su inna, yanzu nan dukkan cin kashi dacin zarafin dataitama su Ai'sha musammanma ita shine zata lullu6e bak'in mugun halinta ta wanketa da alkairin mijinta Dana y'ay'anta? Wace irin k'yak'yk'awar zuciyace da wannan baiwa haka?. Munsha kukan tausayin su innarmu, sannan munyi murna matuk'a da tarbar da akai musu damu kanmu, Su Abdurraheem dasu Aiyaan, da Aryaan, Ahmad, dake k'anan duk an janyesu, kowa yana d'aukarsu cikeda tsantsar so da k'auna. Saida akad'an lafa sannan Sarki yay bayani cikin nutsuwa da dattako. “Lale marhabin agareku y'an uwana, kun kafa tarihin da tilasne a yaba muku, Dan babu wasu da suka sake waiwayen wannan masarauta bayan korar da akaimusu, sun tafi ba'a kuma jin labarinsuba ko inda suke. Bak'aramin durk'usar da wannan masarauta waccan Mummunar Al'ada tayiba, mun rasa ahalinmu masu d'inbin yawa, masarauta dake cikeda dangi yau takoma sai tsirarune a cikinta, kunganmu nan dudu iyakarmu kenan muka rage, wasu sarautunma sai hannun jama'ar gari da bayi ta koma, saboda babu masu rik'ewar, haihuwa itace yad'o, mukuma mun nisanta kanmu da wannan yad'on, masarautar nan ta dad'e tana korar ahalinta saboda haihuwar y'ay'a mata, ALLAH kuma yayta jarabtarmu da samunsu a matsayin y'ay'a, bayan shud'ewar marigayi Sarki Madou Amadi sarakuna kusan 20 sun shud'e a dalilin hakan, bamusan duniyar da sukeba, saida mahaifina yahau ya tsaida wannan al'adar gaba d'ayanta, saboda ganin wataran lallai sai kowa dake cikin ahalinmu ya k'are inhar wannan al'adar tacigaba da wakana, muna baku hak'uri, muna kuma Baku hak'uri, a yanzu wannan masarautar ba ita bace waccan da kukasani, mace Nada daraja sosai a yanzu, tanada kima da k'arfin fad'a aji, muna fata bazaku sake nisantarmu ba, zakuzo mu had'a k'arfi da k'arfe wajen kuma samun yad'uwar wannan masarauta ”. Innarmu da mama Rabi'a Na hawaye suka amsa masa da insha ALLAH. Zayyana muku farincikin daya cigaba da gudana 6ata lokacine, mun shige cikin dangin mahaifanmu munata warkajami, kulawa ake bamu ta musamman da birgewa, aranar aka canja mana masauki Na musamman dayafi wancan k'awatuwa da komai, aka zuba mana hadimai masu hidima, su Abba kam ko ganinsuma bakayi, gagarumin biki Na musamman aka shiga shiryawa Na murnar dawowar su innarmu. Kai lallai munashan kallo, kukadai najin dad'i da farinciki mun shashi, INA y'an gidanmu? Suzo suga abin al'ajabi daban mamaki, innaro dai baki ya mutu murus, saima dukta tsangwami kanta a cikinmu, aiko mukaita zuba mata habaici muma, Dan ganin su innarmu yama gagareta gaba d'aya, sun shige cikin y'an uwansu tamkar dama ciki suka taso, duk wannan hidima batasani mantawa da kewar mijinaba, musamman da Saurayin jiya yafara takurani da kallon tsiya har a ranar, nikuma ban daina antaya masa hararaba, saida nagaji nake sanarma su Munubiya, suma sukace ai duk hakan yake musu, itadai Munubiya tasamu tayi maganinsa ta hanyar mak'alk'alema mijinta, dukda kuma suna tare da Yaa Marwan d'in duk inda yasa k'afa, hasalima Yaa marwan ya koma sashensa gaba d'aya. Daganan tasamu lafiya, saiya koma kanmu ni da Ayusher, dukda wani lokacin yakan Gaza banbantamu ni da Munubiya, inhar baya ganta tare da yaa Marwan bane, itakuma Ayusher ta fini jiki, musamman ma ramar danayi ta jiyyar Dana sha, ita kanta Munubiya tafini jiki a yanzu. Gashi su Abdurrahman sun gagareni d'auka balle nima Na fahimtar dashi inada aure, inkin gansu a wajena shayar dasu zanyi, tokuma bazan iya hakan agabansa ba. Wannan saurayi dai d'ane ga Sarki, Dan shine magajin masarautar ma yanzu. ___________________________ Muna zaune awata rumfar Bunu a washe garin da muka cika kwanaki buyu a masarautar, ranarda za'a gudanar da bikin dawowar su innarmu, zaune muke da wasu y'anmata kusan 8 masu kama damu, duk kuma bazasu wuce sa'annninmu ba, saidai wane ya girmi wane da wata 1 ko biyu, hira muke cikin so da k'auna juna, da d'okin kasantuwarmu ahali d'aya. Suna bamu labarin yanda bikin al'adunsu ke gudana irinsu bikin sallah dana aure, muma muna basu namu, saidai maganar gaskiya ni hankalina ya rabune gida biyu, rabi garesu rabi ga Galadima. Munubiya ce ta lura da hakan, ta d'an ta6ani Na juyo Na kalleta. “Sweetheart mike faruwane wai?”. Cikin marairaicewa nace, “Munu Galadima mana, yakamata yajini koda a wayane, kinga anama mahaifinsa Magani, baikamata ace koyaya bana bibiyar lamarin Yaya lafiyarsaba, karyaga kamar ban damubama”. Cikin gamsuwa tace, “zancenki gaskiyane, shiyyasa kike burgeni wajen hangen nesa, inaga yakamata mu nemi sim card mu saya”. Naji dad'in shawararta, Dan haka muka tambayi y'an matan. 'Daya a cikinsu mai suna Badeera tace, “yanzunan kunason yin amfani da waya shine bazaku kar6i namuba? Amma bamuji dad'iba gaskiya, Ashe bamu zama d'ayanba kenan?”. Hak'uri muka basu, Maryamu ta d'oramin wayarta a jiki tana fad'in gashi kiyi kiran duk Wanda zaki kira, bara a sanarma Yareema issifa yasa akawo muku. (Nayi amfani da namune saboda wasu dalilai, yarenmu ba d'ayaba Dan haka abubuwan da suke fad'a bazai zama d'aya da namuba, to amma Raina kama anginashine bisa wani bigire daban, zanyi amfani da iya abinda Na sani, Dan ban zurfafa bincikeba gaskiya, ALLAH yasa zaku fahimceni😅🤝🏻). Da mamaki nace, “waye hakan?”. Cikin dariya sukace magajin wannan masarautar mana, Wanda kike k'orafin ya dameku da kallo”. Baki nad'an ta6e cikin mamaki, nace, “To wai Issifa sunane?”. Nanma dariyar sukayi, Dijahma tace Youseefa kenan fa. Nace, “tab, sunayenku kukam wasu iri wlhy, nidai bara kuga naje Na nemo mijina”. Dariya duk suka sanyamin. Natashi zuwa cikin masaukinmu. d'akinmu Na shiga, Na lalubo wayata a handbag wadda tunda mukazo suka zama marasa amfani agaremu. ************************** A 6angaren Galadima kam suma Alhmdllh, Abie yanata samun kulawa ta musamman ga Dr Erfan Fahad, Dan da iya k'yautatawar yakema Abie abu, kodan sanayyar dake tsakaninsa da Galadima wadda saidaga baya ya tuna wanene Erfan Fahad d'in, sunyi karatun addni wajen malami d'aya a time d'in bazasu wuci shekaru 9 ba, har lokacin da suka kai 17years shi Erfan Fahad iyayensa suka d'aukesa daga wajen Sheaik Mu'azzam Abdul-aziz, saboda zasu koma Kashmir a lokacin, dama aikine yakawo mahaifinsa India, tundaga nan basu sake had'uwa ba sai yanzun, lokacinda Sheaik Mu'azzam Abdul-aziz ya rasu shi Dr Erfan Fahad yazo gaisuwa, amma basu had'u da Galadima ba, a sanann shikuma yana k'asarJapan karatun shekara 2 daya kaisa, saida ya dawonema yakejin rasuwar malamin nasu, gaisuwa kawai yaje yayma iyalansa yaymusu alk'airi mai yawa. A kullum Dr Erfan Fahad da Galadima cikin hirar tuna baya suke, balle da Dr Erfan Fahad ya d'ebo masa wasu hotunansu suka gani, nanfa suka kuma rikicewa da labari, suna hirar sauran abokansu da rashinjin da sukayi a makarantar. Rabonsa da jin Munaya tun randa suka tafi, suna gab da shiga Niger sukayi waya, daga nan basu sake ba, sosai yake kewarta, duk ya damu, kwana biyu kawai dabai jitaba, har Dr Erfan Fahad saida ya fahimci yana cikin damuwa, Dan Dr Akash da Dr Ajay sun koma India kan aikinsu. Amma Galadima yace masa babu komai, Dr Erfan Fahad bai yardaba, Dan haka ya damesa da tambaya, doledai Galadima ya sanar masa. Aiko ya tasashi gaba da tsokanar wai yace dai soyayya kecin zuciyarsa ba wani abuba, to yarage damuwa, yasan itama laila d'in nacan cikin damuwar rashinsa. Murmushi kawai Galadima yayi, Dan yafara sabawa da yawan tsokana irinta Dr Erfan Fahad, akoda yaushe yanzu suna tare, idan kin gansu ba tareba to yashiga aikine, yakanbar Galadima a Office, Dan har yanzu ba'a shiga wajen Abie, awata na'ura suka sakashi dake taimakama ga66ansa motsawa a hankali, saboda allurar da ake masa duk bayan awanni 12, a koda yaushe saidai Galadima ya lek'ashi ta Window idonsa yakan cika da hawaye, Dan lallai ALLAH ne kawai zaima Abie hisabi dasu Alhaji Lawan tanderu bawai Alk'alin duniyaba. Su Momma sunso zuwa amma Galadima ya dakatar dasu, Dan bayason suzo su d'orama Dr Erfan Fahad nauyi, shikuma maganar gaskiya a tsakaninnan aljihunsa yayi k'asa, damma akwai madogara Na business kala-kala da koyaya asiri zai rufu. Yauma suna asibitin, Dr Erfan Fahad ya shiga wani aiki, Galadima ne kawai zaune a office d'in cikin k'ananun kaya, yana zaune a kujerun dake cikin office d'in daga can gefe, k'afarsa hard'e bisa teble d'in tsakkiyar kujerun, ya d'ora laptop yanata aikin Company daya zamana saita nan, harma Na Hukumarsu dake nan Nigeria, wato (DSS). Idonsa Na saye cikin medical eyeglasses mai haske, sosai yayi zurfi a aikin, alokacinne kiran Munaya ya shigo wayarsa, amma yay burus yacigaba da aikin tamkarma baijiba harta yanke, kuma kira Munaya tayi, nanma yak'i d'auka. Bata gajiba tacigaba da damunsa, cikeda jin haushi ya kalli wayar yana jan tsaki, mamaki ya kamashi ganin Number d'in dabai saniba, baima ta6a ganiba, yanzunma harta yanke bai d'aukaba. Idon Munaya harya fara tara kwalla. Cikeda Damuwa takuma kira, shikuma ya d'auka cikeda k'uluwar an dameshi. Kawai saita sakar masa kuka. Kasa motsawa yayi, Ya kuma kasa magana, Munaya tace, “Ni zakama wulak'anci ko? Shikenan sai anjima”. Zaiyi magana k'itt ta yanke wayar. Kansa ya dafe yana fad'in “O ALLAH my mata bansan ke baceba”. Kiranta yayi amma tak'i d'auka harta tsinke, saida yakuma kira sannan ta d'aga, itama tana gab da katsewar, harma ya fidda ran bazata d'agaba. “Shikenan kin rama ko?”. Ya fad'a a hankali cikin taushin murya da nuna kulawa a gareta. Munaya ta d'an tura baki kamar tana ganinsa, amma batace komaiba. Ya murmusa yana ajiye lap-top d'in ya sauke k'afafunsa. “Kinga bara Na kiraki video call, gara naga dai ma ya kika koma”. Bai jira cewata ba ya yanke wayar. Dad'i sosai ya kamani da jin k'arin k'aunarsa, Wanda ban ta6a tunanin kalloma zan isheshiba shine yake damuwa idan Na damu.......... Kiran ya katsemin tunani, Na d'aga amma saina saka hannuna Na kare idona, bakina da rabin hancina kawai yake gani. “Haba my mata please mana, ko saina miki kukane?”. bakina nad'an motsa da turashi gaba kad'an alamar eh. “Humm kinga duk randa Na kama bakinnan zai min bayani dalla-dallane”. Cire hannuna nai babu shiri ina kallonsa, ya kashemin ido d'aya. Nai k'asa da idona ina fad'in, “ALLAH ya shiryaka, nidai babu ruwana”. K'asaitaccen murmushinsa yayi yana gyara zamansa, “Anya kina missing d'ina kuwa?”. Fuska Na marairaice masa kalar tausayi, nace, “sosaima kuwa”. “uhmyim to inga idon”. d'an kwalina naja Na rufe fusakata ina dariya. Yace, “Nifa wannan kunyar a ringa ajiyemin ita gefe sai ina buk'atarta, ina my children's?”. “Nayi k'yautarsu”. Nayi maganar ina bud'e fuska. “Dakin birgeni, kinga danazo tun anan saina tanajin wasu abin cikin kwan”. Share zancen nai kamar ban fahimtaba, nace, “yaushene zakazo to?”. “Kina missing d'inane?”. “Sosaima ALLAH kuwa”. Dad'i ya kamashi, cikin lumshe idanu yace, “ina tafe soon, sai kunyi kwana 5 sannan zazo nayi kwana 1 mu dawo Nigeria ki tattaro kayanki miyo gaba”. “To ALLAH ya kaimu, ya jikin Abiena?”. “Abienki nata samun kulawa Alhmdllh, muna kuma hango nasara sosai, Dan Abokina yasan aikinsa sosai ”. “Alhmdllh, ALLAH yasa iyakar wahalarce tazo, muma muga Abie d'inmu Na tafiya da k'afafunsa, yadawo k'asarsa ta haihuwa inda mak'iya basa son zamansa, bak'inciki dukya kashe shegu”. “ALLAH ya tabbatar my Queen, guntsamin mana, Yaya kuka iske Niger d'in?”. Cikin tsumud'i nace, “karkad'e kunnenka kasha labari yalla6ai”. “Na karkad'e da k'yau yalla6iya”. Cikin Nutsuwa Munaya ta shiga zayyane masa komai, tun yana al'ajabi yakoma mamaki, Yakoma tausayi, ya koma murna da nuna tsantsar farinciki. Yace, “ALLAH Sarki innarmu, Ashe ita jinin girmace, shiyyasa ta kasance mai dattako, lallai yanzu Na fahimci ina kika kwaso halinnan naki, dama nadad'e ina tunanin anya baki shafi jinin masu sarauta ba, jan ajinki da son girma yayi yawa”. “kai ba'ace naka yayi yawaba sai nawa?”. Murmusa yay yana shafa girarsa d'aya. Yace, “toni minayi kuma?”. “Ai idan zan lissafo maka sai kud'inka sun k'are ban gamaba”. “Sheri dai zakimin kawai yalla6iya, inasu Abdurrahman wai?”. “Tab ai wad'annan inba yunwa sukejiba ganin su wahala yakemin ni kaina, ai saikazo kawai kadai sha mamaki, duk yanda zan musalta maka a yanzu hasashe kawai zakayi”. “Ina tafe insha ALLAH, koma Dan Na d'akko matata Na gudo, amma yanzu kam dole saina nema izinin shigowa”. “Meyasa?”. “Kinta6a ganin jinin mulki yashiga wata masarauta bada neman izini ba? Hakan tilas ne, yak'e-yak'en dake faruwa a masarautu yakawo wannan sharad'in, zuwa yanzu kuma yazama babbar Al'ada mai k'yau”. “Lallai, to yanzu tayaya zaka nemi izinin?”. “Zaki gani bari lokaci dai yayi. Yanzu mizan samu Na rage zafi?”. Cikin salon narkar dashi Munaya ta juya idanu tana fad'in “Mikakeso?”. “Gaba d'ayanki wlhy”. Ya fad'a cikin marairaicewa. “Indai nice dama takace ai Muhammad Sameer”. Lumshe idanunsa yayi yana cije lips, yaune ranar farko daya ta6ajin sunansa a bakinta, “Please sake fad'a naji”. “Mid'in?”. ‘Nafad'a cikin d'an waro idanu’. Ya wani marairaicemin kamar k'aramin yaro, yana k'ank'ance idanunsa da suka sauya kala. Yace, “Sunana”. Yanda yay maganar cikin sanyi da kasala saida tsigar jikina ta tashi, kamar yanda ya buk'ata nakuma maimaita masa a kasalance. “My Queen ina k'aunarki da yawa, zan tabbatar miki hakan randa kika dawo gareni, jinake duk duniya nafi sauran maza morewa da samun nutsatstsiyar mace mai tarin baiwa da tarbiyya, Har abada Na mallaka miki Muhammad Sameer da komai nashi, ki yi yanda kikeso dani my Heartbeat”. Kwallan farin ciki ya cikamin ido. Nace, “My king tukwiycin wannan k'yauta sai ina kusa dakai, Dan tsadarta yakai tsada, tukwiycinta mai girman darajane, kuma zan mik'ashine gamai daraja, dolene yakasance a waje mai daraja, ba Kaine kaima sauran maza zarraba, nice, ni Munaya ninaima sauran mata fintinkau wajen yin dace da samunka a matsayin miji, Uban y'ay'ana, Masoyina, cikon farincikina, I love you so more irin wadda bata k'arewa d'innan har a Aljanna....” “Na gode Uwargidana a Duniya da Aljanna, kece shugabar Matan Muhammad Sameer anan duniya, kuma kece a Aljanna insha ALLAH, ALLAH yayi miki albarka wadda bata yankewa keda gudan jinina”. Hannuna naima kisses uku Na hura masa. Ya wani lumshe idanu yana dafe k'irjinsa alamar sak'ona ya isa. Wata dariya mai ida kashe jiki murus nayi masa, aiko saiya zame ya kwanta kawai cikin kujerar yana kifa wayar a k'irjinsa ya lumshe ido. Nakuma bashi wani kiss d'in mai k'arar sauti, babu shiri ya d'auki wayar da Sauri saidai kitt Na yanke kiran ina dariya. Nima zubewa nayi a gadon k'irjinna Na dukan goma-goma, dayasan tsiyar da Na shirya masa dabai yarda dani hakaba😂🤭. Dariya kawai da tafi naji akaina, nai saurin bud'e ido, sainaga Ayusher, Munubiya, da Feena akaina. Hararsu nayi ina juya fuska can gefe da fad'in, “y'an sa ido, Uwarmiye aka biyoni?”. Ayusher tace, “Yo k'arshen munafurci da cika baki mukazo gani, yaudai munga abinda ake 6oye mana da cika baki”. Suka kwashe da dariya suna tafawa. Banza namusu. Feena tace, “Aini wlhy dama tun a asibiti nace muku gayunnanfa sun d'inke, wuya tayi wuya SIRRIN ZUCIYA ya fito fili, sun gama cika bakin da jan ajin, shi k'asaita da mulki, ita jan aji, Ashe harda Mulkin bamu saniba. Kai kusamana wak'a muyi murnan K'ulluwar k'auna”. Ayusher ta saka wak'a a waya suka ko dage suna tik'ar rawa.. Dariya suka bani wlhy, nace, “y'an iska kwadaiji da munafurcinku wlhy, nan gani nan bari dai Munafuncin su innaro”.. Aiko mi zamuyi inba dariyaba gaba d'ayanmu, nikaina Innaro d'ince kawai tazomin abaki ban shiryaba. ************************** Washe gari aka gudanar da bikin tarbarmu, Wanda yay matuk'ar k'ayatar damu da sakamu farinciki, munga al'adun daba namuba, su innarmu ansha shiga ta alfarma suda su Abba, Saiga su Abbanmu da sarauta, wai tunda sune mazajensu innarmu anbasu wata sarauta domin girmamawa agaresu, hakama Yaa Marwan, dad'i tamkar zai kashemu, aiko munsha hotuna da nuniya wajen jama'a. Gashi ni banda ma sakewa, saboda yanzu banason hayaniya mai tsanani kusa dani, da za'ayi kid'a ma sai wajen nabari tilas, dama hayaniyar mutane da surutai harta fara sakani ciwon kai. Da Galadima ya kirama sai Munubiya ce ta kar6a, ta sanar masa halin danake ciki, duk saiya rikice, yaringa rok'on Munubiya ta kula masa dani sosai. **************** Kwanakinmu 7 da zuwa cif mukaga anata hidimomi a masarautar, kasa shiru mukai saida muka tambayi dalili, su Badeera suka sanar masa wai wani d'an Sarki ne zaizo dana k'asarmu ta Nigeria. Mamaki ya kamani, to wanene wannan? Dan nidai ko a jiya munyi waya da gadima kuma baicemin zaizoba, hasalima yana India, tunanin bashi bane ya sakani kauda zancen araina muka cigaba da hidimominmu. Yanzu kam a masarautar babu inda bamu saniba, Dan kulum su Badeera cikin zagayawa damu suke, har cikin gari saida muka fita sau wajen uku, gaskiya Agadaz tanada abubuwan k'ayatarwa da Tarihi, hotuna kam ai yinsu muke tamkar babu gobe. Su Hajiya Innaro dai kam an nutsu, ni harma tausayi tafara bani wlhy, Dan haka muka rage iskancin da muke mata, yanda ake bata kulawa da girmamata kawai a masarautar ya isheta kunyar abinda ta aikata, (lallai babu Abu mafi dad'i irin ka sakama mai jifanka da sharri da tarin alkairi) wlhy har Abadan bazai sake sukuniba a gabanka saboda d'unbin kunya da nadama dazata addabi zuciyarsa, Dan kullum zai kasance cikin tsarguwa da tsangwamar kansane. Kunga dai yanda innaro ta kasance a yau.😏🤷🏻‍♀ Sai wajen la'asar sakaliya labari yazo mana wai d'an Sarki nan ya iso, bushe-bushen algaitu irin nasu kawai dake tashi ya tabbatar mana da lallai yazo d'in. Cikin mu babu Wanda ya maida hankali akan lamarin, danni kwance ma nake Na kifa Absurraheem saman cikina yana barci, Feena da Deejahma suna gefena zauna suna kallon hotunan da mukayo ayawon jiya da muka fita, su Munubiya kam Na tsakar d'akin suna hira da sauran y'ammatan, Ayusher nama Zuhuriyya kitso, Wanda anayi yana warwarewa saboda gashin akwai santsi, sai wata dabara sukeyi a k'arshen kitson. Bayan sallar isha'i saiga mama Rabi'a ta shigo d'akin da muke, duk muka gaidata, fuskarta d'auke da Murmushi ta kalleni ina canjama Amaturrahman kayan barci dan an musu wanka. “Munaya ta shi kiyi wanka yanzunan”. Da mamaki nace, “wanka kuma mama? Lafiya kuwa?”. “Lafiya lau, kedai ta shi kiyi, bama Maryamu ta k'arasa shirya Amaturrahman d'in”. Nidai duk al'ajabi ya kasheni, ganin duk yawan y'ammatan dake d'akin ba'ace kowa yatashi yay wankaba saini, suma dai Kansu kallon mamaki sukemin ni da mama Rabi'a d'in. Hannuna ta kama muka fice zuwa wani d'akin. Cikin bayin gidan d'aya ta had'amin ruwan wanka, dama tunda mukazo komai yimanashi akeyi. Mama Rabi'a tacemin “Kinutsu kiyi wanka mai k'yau wlhy, inba hakaba dakaina zan canja miki wani”. Mamaki kuma kasheni yayi, nadai nutsu nayi wankan fiyema da yanda take buk'ata, ga ruwa nata tashin mayataccen k'amshi, dan wannan masarauta sunsan sirrin k'amshi kam, akwanaki 7 d'inan har turare yafara zaunawa a jikinmu saboda bala'in yawan amfani dashi, motsi kad'an sai ahau tiraraki da turarurruka iri-iri. Nafito Na iske Ayusher Na jirana wai zatamin kwalliya, zanyi gardama saiga mama Rabi'a ta shigi, dole Na zauna akamin simple, nikaina nasan nayi k'yau, kayan da aka bani Na sanya saida Na kallesu Na sake kallo, dan lafayarsuce ta buzaye datasha wani d'inki mai k'ayatarwa, aka d'oramin bak'ar alk'yabba tamkar ta larabawa, tasha golden d'in aiki daga sama har k'asa, a bud'e take dawasu igiyoyi biyu, can sama dakuma tsakkiya. Nidai narasa bakin magana, dan turarema har neman hawarmin kai ya fara, kai nidai a raina nafara tunanin ko tsafi za'ayi danine. Sai gulma muke da idanu ni da Ayusher, dan babu damar yi a fili ga mama Rabi'a a d'akin. Hannuna ta kama muka fito, aka had'ani da bayi uku nabin bayana, sai ta hud'un a gabana tana mana jagora, masarautar tayi tsit babu yawan hayaniya, saboda d'an Karen sanyi da ake zubawa, kowa ya shige ciki sai d'ai-d'aiku dake kai kawo. Wani sashe dakecan gefe shima mai k'yau muka Isa, munsha zuwa ta wajen amma bamu ta6a shiga cikiba, Baiwar tayi sallama, dukda ba'a amsaba ta shiga, mukuma muka cigaba dabin bayanta. K'aton falone mai tarin k'awa da tsari, Wanda ke tabbatar maka a gidan sarauta kake, ganinai duksun durk'ushe k'asa, Na bisu da kallon mamaki sannan Na kalli inda suke fuskanta...................✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [8/15, 6:54 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣4⃣ .................A hakimce yake kishingid'e saman lallausan dardumar data k'awata k'yawun falon, Rabin jikinsa duk akan tum-tum, gabansa da butar shayi ta buzayen asali, gakuma mitsi-mitsin kofuna saman wani k'yak'yk'yawan tire k'arami, gefe Bowl ne Na glass cikeda kayan itatuwa, saikuma kwanika 4 dake rufe Wanda bansan minene a cikiba, gefensa yaransa ne duka ukun kwance duk nad'e cikin showals, yanda nake binsa da kallon mamaki haka shima yake bina da kallon mamakin canjawa da k'ayatarwar da shigar ta k'aramin. Sudai bayinnan sun lalla6a tuni sun fice abinsu. Cikin d'age gira ya sakarmin Murmushi yana min nuni da hannu wai nazo gareshi. Tamkar mai tsoron a kamata tana satar naman miya haka nake tafiya garesa, dan kallon da yakemin ba k'aramin haddasamin kasala da sanyin jiki yayiba. Na k'arasa gabansa ina zama a kasalance, zaman danayi ya kalla, ya min jinjina irinta saraki👍🏻. Kallon kaina nayi nima, dan banga minayi ba dahar za'amin wannan jinjinar. Cikeda k'asaitarnan tasa yace, “Kallon fa?”. Ajiyar zuciya Na sauke, dan narasa bakin magana, ya tashi zaune sosai yana janye tum-tum d'in dake a tsakkiyarmu, ya matso jikina sosai yana wani shinshinata da lumshe idanu, murya a sark'e yace, “Amaryar Muhammad Sameer wannan k'amshin yayifa 100%”. Yanda yay maganar a dokin wuyana saida tsigar jikina ta tashi, cikin magana d'ai-d'ai nace, “Wai dama Kaine d'an Sarki da aketama wannan shirin?”. Murmushi ya saki, ya matsar da bakinsa saitin kunnena a wani salo yace, “koban cancantaba ne?”. Kaina Na girgiza masa alamar a'a. Ya kuma shigewa jikina sosai, “Wai miya kashe bakin tsiwarne haka yau?”. “Mamaki mana”. “To miye abin mamakin? Ni d'in ko zuwan nawa?”. Nace, “Duka”. Wani miskilin murmushi ya saki, ya lalubo hannuna dake 6oye cikin alk'yabbar ya saka nashi ciki yana murzawa da wani salo, juyawa nayi Na kallesa muka had'a ido, idanunsa duksun wani k'ank'ance, ya sark'e nawa yanda nakasa koda motsi balle samun damar janyewa, akan la66ansa yace, “I miss you”. “Humm” nafad'a nima a hankali INA kauda kaina gefe. Hannunsa ya sak'alo ta bayan wuyana ya matso da fuskata dab da tashi, numfashinmu Na had'uwa waje d'aya, kasa jurar kallonsa nayi saina lumshe idonuna Na bamik'a masa wuya 100%, yayi duk yanda yakeso, dan da gaske missing d'in nawa mai yawa Nagano cikin kwayoyin idanunsa. Da sauri yarima Issufu da Yaa Marwan suka koma baya, dan dama suna tare da shine aka aiko kiransu, sunata sauri su dawo dan karsu barshi cikin kad'aici, ashema yana tare da matarsa. Sunyi sallama takai 6 jin ba'a amsaba sukayi tunanin kobaijibane, shiyyasa suka shigo Kansu tsaye, dan basuyi zaton samunsa da kowaba, ALLAH ma ya sosu k'aramin gani sukayi🤭😂. Yareema Isaufu da mamaki ya kasheshi ya kalli Yaa Marwan yana fad'in, “wai dama duk yarannan masu kama da juna sunada aure?”. Murmushi Yaa Marwan yayi, ya dafa kafad'arsa, “biyu sunada aure mana, su tagwayene, ina auren Hasaanar, shikuma Yarima Sameer yana auren Hussaina, d'ayar itace bata da aure, dan nasan Ayusher kake nufi, tunda Feena bata kaisu girma da shekaruba, amma miyasa kamin wannan tambayar?”. Yareema Issufu yay k'aramar dariya yana cewa “zan sanar maka amma ba yanzunba, saida safe Na banbancesu”. Komai Yaa Marwan baiceba yay murmushi kawai suka cigaba da tafiya. Mukan bama musan sun shigoba balle fitarsu, motsawar da Abdurrahman yayi yana k'ananun kukane yasamu dai-daita, duk muka kalli inda suke. Matsawa Galadima yayi inda suke dan sunfi kusa dashi, Ashe showal d'inne ya rufe masa hanci, ya gyara masa sannan ya juyo ya kalleni yana murmushi. K'asa nayi da kaina nima ina murmushin. Nace, “Ina yini? Kazo lafiya?”. “Kin fita daga mamakin yanzu dai kenan?”. Yay maganar tamkar bayaso. Nanma Murmusawa nayi ina 6oye fuskata. “Humm”. Ya fad'a yana gyara zama. “Kayannan sun miki k'yau gaskiya my mata”. Nad'an d'ago ina fad'in, “Da gaske?”. Ido d'aya ya kashemin yana cizar lips. Nima Na juya idanuna cikeda salo. Har cikin ransa saida yaji wannan sak'on. Na katse masa tunanin da fad'in “Ya jikin Abie?”. Zamansa ya gyara sosai, ya d'auki butar shayin zai zuba nai saurin d'aura hannuna akan nasa ina girgiza kai. “Aikin ai nawane yalla6ai”. Murmusawa yayi yana sakarmin. Nima Na zuba masa fuskata d'auke da Murmushi, Na mik'a masa. Cikin lumshe idanu yace, “Thanks”. Kaina Na jinjina masa kawai, a nutse ya shiga bani labarin dukkan abinda ya faru, harda tsadar allurai da drugs d'in da Abie kesha, ya k'are maganar da fad'in ammafa Alhmdllh, bazan baki labarin komaiba sai kinje kinganema idonki yanda Abie yake yanzu, banta6a tafiya mai cike da nutsuwa ba irinta wannan karon, dan nasan nabaro farin ciki ne zan kuma iske farin ciki, lallai Na yarda da zancenki, HAK'URI shike bada komai, duk saurin Bawa saiya jirayi UBANGIJI, dan shine mai kowa da komai, a watanni biyu kacal da suka shud'e ganinake komai ma bazai zoba balle ya wuce, amma gashi harya zama labari, wataran muma masu bada labarin nemarmu za'ayi a rasa, mun shud'e saidai bayanmu, ALLAH ka rabamu da SON ZUCIYA, dan k'arshedai 6ACINTA, Ko'a yanzu akace babu Muhammad Sameer to naci ribar rayuwa, dan burina nason ganin mak'iyan mahaifina ya cika, Abie yasamu sauk'i, ga yarana, Na mallaki jarumar mace kamila Mumina wadda Na mallakama dukkan kaina da ZUCIYATA, To nikam minene ya ragemin kuma MATATA!?”. 'Dago idanuna dake cike da kwalla nai ina kallonsa, a hankali nace, “Sai addu'ar samun aljanna my King”. Ya lumshe idanunsa yana murmushin daba koyaushe yake yinsaba yana min jinjina 👍🏻. Nima na jinjina masa ina k'aramar dariya. Muncigaba da hirarmu a tsanake cikin so da k'auna da nunama juna kulawa. Yauma langaremin yayi saida nabashi abinci da kaina yaci, nima dai haka ya ciyar dani da kansa. Ban bar sashenba sai wajen 12, shima su Yaa Marwan muka tausayamawa, dukda kowa da d'akinsa, falone kawai ya had'asu. Da kansa ya d'akkomin Absurraheem da Amaturrahman, ya rakoni, aiko muna fitowa yace, “ya salam, my mata dama haka wajennan keda sanyi?”. Cikin tausayawa Na kallesa, dan nima Na manta kayan dake jikinsa k'ananune, dan ciki akwai d'umi sosai, bama zaka tuna ana sanyiba, “kawosu kawai ka koma, kar mura ta kamaka”. “No muje da sauri Na rakaki, dan sunmiki yawa ai”. Har k'ofar sashen da muke ya min rakkiya, Na lek'a Na kira Wanda ke kusa danya taimaka min, Ayusher Ce ta fito itada Zuhuriyya, Na kar6esu d'ai-d'ai daga wajensa ina mik'a musu, yayinda suke gaisheshi sukuma yana amsawa da kulawa. Suna shigewa ya jawoni jikinsa, waige-waige Na fara dan gudun kar wani ya gammu, shikam ko'a jikinsa, ya mannani da gini yana yanda yaso, kusan mintuna 2 sannan ya sakeni yana fad'in “Good night”. A hankali tare da d'agamin yatsunsa biyu. Kasa magana nayi harya 6acema ganina, Na sauke ajiyar zuciya ina shiga ciki a sanyaye tamkar wadda tama sarki k'arya. Duk sunyi barci, sai Ayusher da Maryamu da Zuhuriyya ne kawai ido biyu, sai bina da wani kallon tuhuma suke. Na zauna ina fad'in, “waiku lafiya kukemin kallon har hanji?”. Dariya suka sanyamin, Ayusher tace, “Hajiyata ina janbakin Dana Sanya miki?”. Harara Na zuba mata nace, “oho miki sa idiniyya”. Natashi nai shigewata. Aiko mizasuyi inba dariyaba, nima Na shige ina k'unshe tawa. Shirin barci nayi nai kwanciyata, har suka shigo suka kwantar da yaran ban kulasuba saima nayi tamkar barci nakeyi. Dama Laraba Na iske tayi barci abinta ita tuni, Na dad'e banyi barciba, kasancewata tare da Galadima ta tsayamin arai, kai wannan Bawa akwai iya salon d'auke zuciya iri-iri, duk hanyar dazaibi ya dabaibayeki ya Sani. Shima a 6angaren Galadima da k'yar yay barci, da badan kar ace yayi abin kunyaba da babu inda matarsa zata ta barsa, yana buk'atarta a kusadashi ainun, amma ya zaiyi, dolene ya had'iye kwad'ayinsa harsu dawo kusa dashi. Haka yayta juye-juye harya samu barci ya d'aukesa. *_Washe gari_* Ban samu damar ganin Galadima ba har a zuhur, dama gashi an tashi da sanyin daya hana kowa sukuni, sai a waya muka gaisa dashi, bayan Azhur aka kaimasa yaransa dai, sunsha gayu cikin kayan sanyi. Bayan sallar la'asar mukad'an fito ni da sauran y'an uwana domin mud'ansha iska dai, saidai kowa a cikin kayan sanyi yake, ina goye da Meenal, yayinda suma sauran yaran su Badeera duk suka goyasu. Mun shiga sashen matan sarki mun gaishesu mun fito muka had'u da su Galadima sun fito daga masaukinsu zasu shiga mota, da alama dai fita zasuyi. Ido muka had'a dashi ya sakarmin Murmushi da d'agemin gira d'aya. Nima murmushin namasa ina juya idanu. Da yake d'an nesa damu suke, basu zoba muma bamu k'arasaba, suka shiga motar da aka bud'e musu. Har suka fice inabin motar da kallo. ******** Tarbar da Galadima ya samu ta girma da mutuntawa tamasa dad'i ainun, Dan shima har wata sarauta suka bashi, sun Nuna farincikinsu Na had'a jini da babbar masarauta irintasu Galadima, shima kuma yayi farincikin kasancewarsu cikin yankin ahalin matarsa, shikam bashida abun fad'a sai godiya. Washe gari Sarki da Kansa yasa aka kirani, naje har turakarsa Na samesa, nasiha yaymin mai ratsa jiki, ya k'ara nunamin Girman daraja da Kimar masarautar su Galadima dayake gani, dukda basu had'a k'asa d'ayaba, inhar Na aikata k'yak'yk'yawa martabarsu da darajarsu Na kare, domin su ahalinane, kuma dole ace daga tsatsonsu Na fito, Na kare musu mutuncinsu, shima bada dad'ewaba zai shigo Nigeria insha ALLAH. Cikin girmamawa da share hawaye nace, “Insha ALLAH bazan baku kunyaba, zan zama d'iya tagari mai ado da tarbiyyar ahalinta Na kowanne 6angare,, da izinin ALLAH saikunyi alfahari dani”. “ALLAH yayi miki albarka, Yakuma tsareku da dukkannin sharri keda y'an uwanki, yabaku zaman lafiya Na har abadan a gidajen aurenku”. Nace, “Amin Abba mun gode sosai, ALLAH ya k'ara girma”. A gurguje please🤗 ******************* Kwanakin Galadima uku a masarautar muka fara shirin tafiya, dan mura ta kama shi ram, gashi bata masa da sauk'i, a lokacin mu kwanakinmu 10, kowa yana cike da kewar tafiyarmu, jisuke kamar karmu tafi, mu kanmu a kewar rabuwa dasu muke ji sosai, dan Sabone maiban mamaki da shak'uwa ta shiga tsakaninmu, ba k'aramar hidima suka manaba, lamarin harma yayi yawa, sukace suma insha ALLAH suna tafe garemu nan kusa. Mussamman da kowa ya fahimci alak'a mai k'arfi dake tsakanin Yareema Issifu da Ayusher, wadda kowa yake cikin tsantsar farinciki da fatan ALLAH ya tabbatar da wannan had'i. Yanzu kam tafiyar ta canja salo, dan Munubiya da Yaa Marwan, ni da Galadima. Innarmu da Abba, mama Rabi'a da abbansu Ayusher, Feena da Ayusher, innaro, laraba, Yaa Fadeel dasu Aryaan aka had'asu a babbar mota guda d'aya (gwauraye kenan🤭🤣). Tunda Na shigo motar k'amshin turarensa ya faramin sallama, sanye yake cikin milk d'in shadda datasha ainahin aikin masu sarauta harda hula, yayi k'yau, Dan yau a sarakinsa ya fito, muka kalli juna kowa yay murmushi, saida Na zauna sosai su Deejama dake rik'e da yaran suka mik'ominsu, ganin zasumin yawa yad'an matso ya d'auki Abdurraheem da Abadurrahman, idona dukya cika da k'walla, haka suma su Maryamu hawaye sukeyi, haka suka rufemu suna d'aga mana hannu. Saida motar ta fara tafiya sannan hawayena suka sami damar zubowa. Galadima da tun shigowata idonsa Na kaina yay murmushin gefen baki, tissue ya Ciro a bayanmu ya matso jikina sosai da d'ago fuskata. Kallonsa nayi, idanunmu suka sark'e cikin Na juna, ya lumshe nasa dake cike da barci da mura wadda ta k'ara musu girma da canja kalarsu jaa kad'an yana girgizamin kai alamar nabar kuka. Bance komaiba, sai kuma matso hawayen da nayi, yasaka tissue d'in ya gogemin, sannan ya sumbaci saman la66ana kad'an yana jingina kaina da kafad'arsa. Shiru nayi ina sauke ajiyar zuciya kad'an-kad'an, yayinda shikuma yake d'an shafa gefen kafad'ata daya d'oro hannunsa wajen, saida nasami nutsuwa sannan Na d'ago, kallona yayi muka had'a ido, cikin salon rashin son yayi magana ya kad'a kwayar idonsa alamar yadai?. Da hannu Na nuna masa yaran nima, dukda bai fahimci minake nufiba baice komaiba. Hulunan su Amaturrahman Na fiddo a handbag zan saka musu, dan sauri bai barni nayi hakanba dazamu fito, anafa fitowa daga sallar Asubahi akaita mufito-mufito, kuma duk Yaa marwan ne da wannan azalzalar. Amaturrahman dake jikina Na sakamawa, shima gogan da mura taima murus ya kar6a yasakama mazan yana magana tamkar an masa tilas, “kai garinnan da dad'in zama da wahala, wannan sanyin nikam shiya hanani sukuni”. Dariyar data tahomin Na had'iye da k'yar ina fad'in “Ai sanyin kam babu sauk'i, sunce idan zafima yazo yashin yaji rana haka suke azabtuwa, garama sanyin, kaji kuwa muryarka fa ta canja gaba d'aya”. Murmushi yayi ya jingina kansa dake masa ciwo jikin seat batareda ya amsaminba. Nima sai ban sake magana ba, Na nad'e yaran sosai a showal dukda glasses d'in duk a rufema suke, driver dai nata tuk'insa, ni idan son samunema Na kwanta, Dan barci nakeji sosai, jiya bamuyi wani barcin kirkiba anata hirar bankwana, muna kwanciya babu dad'ewa innaro tafara tashinmu mu shirya. Seat d'in gaba Na kalla, tunanin maida yaran can yazomin, nakuwa d'aukesu d'ai-d'ai ina maidawa, tunda suna cikin kayan sanyi, kuma barcinsu sukesha, nima ai saina huta ko. Zamewa nayi Na kwanta tareda d'ora kaina a cinyarsa, ido kad'an ya bud'e ya kalleni da mamaki, “Ina yaran?” ya fad'a yana kallona. Da hannu Na nuna masa gaban motar, “Amma ai zasu takura a can?”. A shagwa6e nace, “ALLAH bazasu takuraba, barci nakeji har kaina yafara ciwo”. Kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru, Dan bayason yawan maganar saboda kansa ciwo yake sosai. Nima ban sake cewa komaiba Na gyara kwanciyata ina lumshe ido, hannunsa ya d'ora a jikina daganan motar ta d'auki shiru, Dan barci tuni yayi awon gaba dani, shima a hakan barcin ya kwasheshi. Bamu kuma sanin halin da ake cikiba saida tafiya tai nisa sosai, yara suka farka suna k'ananun kuka, shine ya fara farkawa, ya bud'e ido a hankali bakinsa d'auke da addu'a, agogon hannunsa yafara kallo, sannan ya maida kaina danabi dukna kanainayeshi, yad'an murmusa yana janye gyalen jallabiyar jikina daya rufe rabin fuskata, barcina nake hankali kwance, shi saima yaga Na k'ara k'yau a hakan. Kukan yaran daya fara k'arfine ya sakashi dawowa hayyacinsa, ya shafa fuskarta a hankali yana kiran sunanta. Munaya batada nauyin barci dama, idanma aka cika surutu a kusa da ita takan farka, tad'anyi mik'a tana bud'e ido, hannunsa nakan fuskata ya zubamin idanu, ni saima kunya ta kamani, naja gyalen Na rufe ina tashi zaune. Murmushi yad'anyi yana fad'in “Duk kin samin ciwon jiki”. Fuskata Na bud'e ina tura baki kad'an da kallon kaina, ina naga nauyin dazan saka masa ciwon jikin?. Fahimtar abinda nakeyi dayayne ya sashi cewa, “kina kokwanto ne?”. Nace, “sosaima”. Nai maganar ina d'akko yaran. Yanzuma kar6ar biyu yayi, Na dungure kan Abadurrahman ina fad'in, “kun ishi mutane da k'ananun kuka, nima yunwar nakeji ai”. Galadima dake kallonmu cikeda sha'awa yay murmushi mai sauti dahar ya bayyana hak'oransa a waje, amma baice komaiba. A nutse Na shayar dasu su duka d'aya bayan d'aya. Munzo cikin babban wani gari Galadima ya Umarci driver da cewar yasama mana wajen abinci mai k'yau, Dan karsu Aiyaan suji yunwa. Cikeda girmamawa driver ya amsa masa. Abinka da driver manya, dukkan wani wajen girma sun sanshi, kansa tsaye ya kaimu wani had'ad'd'en wajen cin abinci, saima kayi gaddamar ba'a Niger d'in yakeba, duk fitowa mukayi, amma Galadima yak'i fita, saida su Abba suka shige sannan, Ayusher da feena sukazo kar6ar yaran, Dan can Yaa Fadeel da Laraba sun kar6i Ameen da Meenal. Mik'ama Ayusher Abadurrahman nayi, Na bud'e inda Galadima yake Na rank'wafo ina d'aukar Abadurraheem, shima mik'ama Feena nayi, itama Amaturrahman Na d'akkota Na rik'e, ganin ko motsi baiyiba nace, “yalla6ai yadai?”. 'Dan yatsinamin fuska yay saikace wani mace. Na kuma rank'wafowa ina d'ora hannuna saman goshinsa, tausayinsa ya kamani, dan kan akwai zafi alamar bayajin dad'i. Nace, “Sorry my king”. Idonsa yad'an lumshe yana murmushi. Nakuma cewa “ka daure muje ciki, sai a nemi maganin mura”. Nanma baice komaiba, saida yaja wasu seconds sannan ya ziro k'afa, nad'an matsa baya nabashi hanya ya fito. A raina dai ina jinjina jinin masu mulki, k'asaita da izza tarigada tazama jinin jikinsu, babu yanda za'ayi ka iya rabasu dashi. Da hannu yayma Drivers d'in alamar su shiga suma. Mune k'arshe. Shiga. ALLAH Sarki Yaa Marwan, harya tanadar mana wajen zama, gaskiya babu k'arya wajen yayi tsari, mukam mund'an shiga daga lungu kad'an, su Abba basa ganinmu bama ganinsu, inaga hakanne yasaka Galadima d'an sakewa yaci abincin, dukda bama wani Na kirki yaciba, Dana nuna damuwa saiya kalleni. “Karfa ki damu, inhar ina mura banajin dad'in komai, haka take wahal dani”. Cikeda tausayawa Na masa sannu, nima duk saina kasa cin abincin. Spoon d'in hannuna ya kar6a, da kansa ya koma bani abaki, dukda marairaice masan da nayi akan Na k'oshi bai saurareniba, baikumayi maganaba, saida ya tabbatar Na k'oshi da gaske sannan ya barni. Kowa yaci ya k'oshi yay nak Alhmdllh, muka fito da ledojin kayan mak'ulashen da Yaa Marwan shima ya saima kowa, dan kud'in abincin Galadima ya biya. Dagananfa muka damk'i hanya babu sanya, dan burinmu mu Isa Nigeria a yau, wancan zuwanma dan bamusan inda muka dosa bane. Aikam dai tafiya tayi riba, dan salla kawai muka tsaya mukayi, Azuhur da la'asar muka had'a muka kuma damk'ar Hanya, bayan magrib muka shigo Nigeria, nanma mun tsaya munyi sallar Magrib da isha'i, daganan muka cigaba, abinci ma sai saya akayi kowa yaci a hanya. Yanzunma dai Galadima baici Na kirkiba, dan bayajin dad'in bakinsa, da gaske Mura batai masa da wasa kam, dam duk bashida wani sukuni. Sai wajen 2am muka shiga namu garin, zuwa lokacin kowa yayi ligif, ga gari tsitt, sai motoci jefi-jefi Na matafiya irinmu, saikuma manyan motoci masu d'aukar kaya. Gidanmu aka nufa, saida aka fara saukemu harsu mama Rabi'a anan, Fadeel Yaa Marwan da Abbansu ne kawai aka nufi gida dasu su kam, shima Galadima masarauta aka juya dashi, sama-sama mukayi sallama Na fita, tausayinsa Na cin zuciyata, yana buk'atar kulawar matarshi matuk'a, amma ya zanyi. Duk y'an gidanmu sunyi barci, sai tsirarune suka fito y'anson ganin dami mukazo?. To babuma abinda aka fitar daga mota, kowa dagashi sai handbag d'insa ya fita. Koda muka shiga kowa wajen kwanciya ya nema, dukda sashen namu yad'anyi k'ura, amma bamu damuba, Inda zamu kwanta kawai muka karkad'e. ***************** Galadima yana shiga gida ruwan zafi ya had'a yay wanka, kozai sami sauk'in ciwon da jikinsa ke masa, yad'anji dama-dama kam, ya nema kayan barci masu kauri ya saka, dan muma dai nand'in cikin sanyin ake, gadonsa ya haye, ya shige bargo yana sauke numfashi da k'yar, babu dad'ewa barci yay awon gaba dashi. *Washe gari* Bamu tashiba sai kusan 12, su innarmu ne kawai suka tashi da wuri, y'an gidanmu anata shigowa musu sannu da zuwa, kowacce jikinta saiya fara zanyi, dan yanda muka dawo 6ul-6ul damu kad'ay ya Isa basu amsar muna cikin k'oshin lafiya, kuma inda mukaje wajene mai daraja. Duk wadda ta fita saita nufi gidan Innaro da nufin mata sannu da zuwa, ammafa dason jiyo gulma. Tab hajiya Innaro mai abin mamaki, zama tayi tiryan-turyan tana basu labarin garar arzik'i da wacece Inna. Ta rik'e ha6a tana tafa hannaye da fad'in “Yo Niko koda naji wannan halin dattako Na Ai'sha, Ashe jinin sarautace , shiyyasa duk shirmenkunan bata shigarsa, maganama saitaso ta kula maiyinta, duk shirme ya rufe mana idanu bamu fahimtaba, lallai yau naga tushen arzik'i Na gaskiya ba hayeba, nayarda da masu iya magana dakance duk Wanda yace shine to bashi bane wlhy.....”. Innaro dai taita zuba musu labari babu k'ak'k'autawa, sukam sun kume motsin kirki summa kasa, a yanda su inna suka dawo kawai ya Isa ya tabbatar musu da gaskiyar innaro d'in. Tunaninsu bai kuma birkicewa ba saida aka shiga fiddo tsaraba daga motocin da muka dawo dasu, kowacce saita shige d'aki ta koma lek'e ta window itada y'ay'anta🤣. Zarah da siyama da har yanzu suna gida, a sanyaye suka shigo gaida su inna, duksun rame sunyi duhu, dan kowacce tana son mijinta, amma gidajensu sun gagaresu komawa, dan bayan tafiyar su Munubiya saiga takardun saki daga mazajensu su duka. Duk munyi mamakin yanda sukai laushi da fita hayyacinsu, amma bamuce komaiba, muka tarbesu kamar yanda muka saba a ko yaushe. Nidai wlhy duksai tausayinsa yama kamani. Su Ayusher sukai shirin tafiya gida, iya abinda zasu iya d'auka suka had'a Yaa Marwan yazo ya kwashesu.. Suna tafiya nima sai hankalina ya koma ga mijina, waya Na d'auka Na kirashi dan naji Yaya jikinsa, harta yanke bai d'agaba, nakuma kira dai... Galadima Na kwance zazza6i ya rufeshi, tunda yay sallar Asubahi yakoma yakuma k'udundunewa a bargo, cikin barci yaji wayarsa Na ring, kasama motsawa yay balle ya d'auka harta tsinke kiran yakuma shigowa, hannunsa ya tura k'ark'ashin filon da k'yar ya jawo wayar, yabud'e ido kenan ta katse, harzai ajiye saikuma yaga my mata, kiranta yay yamaida idonsa ya rufe yana saka wayar a kunne batareda yayi maganaba. A sanyaye Munaya tace, “Yalla6ai are you okey?”. “My Queen!”. Ya kira sunana a hankali ba tareda ya amsa tambayar dana masaba. Sautin muryarsa kawai ya tabbatar min da lallai bashida lafiya har yanzu, rikicewa nai nacigaba da jera masa tambayoyi, babu wadda ya iya amsamin saida yaga nak'i inyi shiru yace, “relax dear, zan samu sauk'i karki damu”. Hawayen da suke zubamin Na share, Na tabbata abinda zai kwantar da Galadima ligif haka ba k'arami bane, inhar yazam ba ciwonsaba to lallai abin ya girmama. K'arasowa innarmu tayi da sauri cikin d'akin d'auke da Amaturrahman dake kuka, dukta rikice ta shiga tambayata lafiya?. Dole Na yanke wayar ina duk'ar dakai da saurin goge hawayena. Nace, “Innarmu shine baida lafiya har yanzun”. “Ya salam, murardai?”. Kaina Na d'aga mata. Amaturrahman ta d'oramin a cinya tana mik'ewa. “To ai bakiga ta zamaba kuwa, bara Na sanarma abbanku”. Ban iya cewa komaiba Na fara shayar da Amaturrahman ina share hawaye. Bansan miya faruba kawai naga Munubiya ta shigo tana had'a kaya, da tambayata ya jikin nasa?. Na amsa mata ne kawai cewar da sauk'i amma badan inada tabbacin hakanba. Itace take sanarmin wai Su Abba sunce muma mu shirya kawai mu koma d'akunanmu tunda andawo lafiya, zaman wankan ya Isa kawai...............✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [8/15, 6:54 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣5⃣ .................Da mamaki Na kalli Munubiya ina kwantar da Amaturrahman. Nace, “Komawafa Munu?”. Tsayawa tayi daga shirya kayan da take tana kallona da mamaki, “Ban ganeba, bakison komawar ne? Dakikemin wannan banzar tambayar?”. Baki Na zum6ura ina fad'in “Nikam dai bazan koma haka siddan ba, sai inhar yazo ya warwarema iyayena komai gameda tubalin daya k'ulla aurenmu a farko, yakuma basu hak'uri”. Kasa magana Munubiya tayi, saima ta zauna a bakin gadon, ita batasan wajen ubanwa Munaya ta d'akko halin taurin kai ba wlhy, ita tama rasa mizata ce mata. Nima d'auke kaina nayi gefe Dan ina kan bakana, ina tausayinsa Dan koba komai ya k'yautatamin a lokacin da nima banida lafiya, kuma ta silata yake kwance yanzu, to ammafa hakan bazai zama yasha a banzaba, kenan ma anan gaba wasu zasu iya aikata hakan ga kowacce mace?. Laraba dataji komai dake faruwa tana niyyar shigowa saita koma da baya gabanta Na fad'uwa, ita bataga laifin Munaya ba, dan wannan shine martaba da sanin ciwon kai, kuma wannan ya tabbatar mata da ba kwad'ayine yasata zama da shiba, amma bata fatan abinda zai girgid'a wannan Auren komai k'ank'antarsa waya ta d'auka ta kira Mom ta sanar mata komai, hankalin mom ya tashi, danba ta wanann hanyar takeson Munaya ta hora Galadima ba, bakuma taso iyayenta su Sani, suma sunada burin d'aukar mata mataki itada Momma, Dan bazasu bar wannan gangancin Na Galadima ya wuce a banzaba.. Momma ta kira tace Dan ALLAH ta kira Munaya tabata hak'uri akan ta koma, Dan babu mai kula da Galadima d'in, insha ALLAHU daga baya wannan maganar za'ayita. Momma ma duksai ta damu, dan har cikin ranta tana k'aunar Munaya, bazataso wata matsala ta tasoba bayan hankalinta ya kwanta akan zamansu. Munaya suna tare da Munubiya har yanzu a d'aki, ta balbaleta da masifa kamar ta daketa, Munubiya tanada hak'uri, shiyyasa idan tana masifa dolene kasan takai k'arshen 6acin rai, Munaya saita zuba mata ido kawai takasa cewa uffan, ana cikin hakane kira ya shigo wayar Munaya. Harzata share saikuma ta d'au tana dubawa, ganin Momma tai saurin d'agawa tana share hawayen da suka zubo mata. Cikeda girmamawa kamar yanda ta saba ta gaisheta. Daga can Momma ta amsa cikin kulawa itama, face, “Kun dawo lafiya d'iyata?”. “Alhmdllh Momma ya jikin Abie”. “Jiki kan Alhmdllh d'iyata, dama Abbanki ne ya kirani akan zaki koma, saboda Muh'd babu lafiya, da farko dai nayi tunanin cewa a barki harsai yazo yafad'a musu laifin daya aikata agaresu, saikuma nayi wani tunani daga baya, kiyi hak'uri ki koma yaud'in Dan ALLAH, saboda Mura bataima Muh'd da sauk'i, namiki alk'awarin zan d'auki mataki da kaina, zan sanar masa Ku tahoma gobe idan ALLAH ya kaimu kinji”. Bazan iyama Momma musuba har abada, Dan nasan bazata cutar daniba, saidai kuma nayi mamakin dama tasan auren Contract mukayine?....... Katsemin tunani tayi da fad'in “d'iyata idan kinga zaki cutu abari kawai, bazan ta6a bari Muh'd ya cutar dakeba wai danni Na haifesa wlhy”. “A'a Momma Na amince”. Daga can Momma ta sauke ajiyar zuciya tana fad'in, “Alhmdllh, d'iyata nagode sosai, ALLAH yay miki albarka kinji”. Idona cike da kwalla Na amsa da amin. Tace Na gaida mata kowa ta Yanke wayar. Munubiya dukda ta fahimci dawa Munaya tayi waya batace da ita uffanba, tacigaba da had'a musu kaya kawai. Ciwonsa ne yasani Na danne zuciyata Na amince, dakuma Kimar mahaifiyarsa danake gani, Dan sun nunamin dukkan k'aunar da inhar Na bitilcemusu banma kaina adalciba nima. yinin ranar gaba d'aya a hidimar shirin komawa mukayisa, ga gajiyar tafiya Na nuk'urk'usarmu, amma ya muka iya, da yamma dole su mama Rabi'a suka dawo domin mana rakiya. A gurguje please🤨😏. ****************** Abin mamaki sai gamu da rusar kuka ni da Munubiya, saikace wasu sabbin amare, bayan nasiha da Abba da baba k'arami, daddy sukai mana Na ajiye musu keys d'in motocinsu, da farko sunce bazasu kar6aba Na sanya musu kuka. Innaro tahau musu fad'a babu k'yau maida hannun k'yauta baya ai, wannan aikin shaid'anne. Albarka dai munshata kam, yayinda zukatan matan gidanmu yakusa babbakewa saboda bak'ar hassadarsu, kowa son samunshi ace d'ansane yayi. Laraba ma harda hawayen sabo, dan bak'aramar girmamawa aka mata a gidannanba, har abada bazata ta6a mantawa da dattako irinna inna ba. Kaf matan gidanmu dasu aka tafi, innarmu da Innaro kawai aka bari, amma hardasu Siyama. Ni suka fara rakawa, ALLAH ya somu muka iske Muftahu yadawo daga yawonsa zai shiga masarautar, da taimakonsa muka shiga, yayi mamakin dawowata, dan Galadima ya sanar masa muna Niger, shi baisan yadawoba ma, hasalima babu Wanda yasan Galadima ya dawo masarautar, tunda ko salla bai fitaba, sai hadimansa kawai. Ba sashenmu akai kainiba, Muftahu ya sanar musu sai an fara kaini wajen mama Fulani sannan, haka al'adar masarautar take. Aikam dai hakan akayi. Tarba ta mutunci mama Fulani tasa akaima dangina, tana nandai yanda kuka Santa da mulkinnan nata da izza, amma ni a yanzu tunda Na fahimci ita ba muguwa bace sai salon nata yake k'ayatar dani. An min dukkan yanda al'adar masaurat ta tanadar, sannan mama Fulani dakanta tamin rakkiya sashena tareda bayi da dangina, ko ina k'al tamkar muna nan. Bayan fitar mama Fulani y'an gidanmu suka kuma shishshiga suna kallo gida wai, dan ranar suna da suka fara zuwa basu sami wannan damarba saboda idon mutane, nidai batasu nakeba, hankalina nakan mijina, burina naje naga halin da yake ciki. Munubiya takuma min nasiha da bani wasu dabaru, tunda su sinzama tsoffin hannu, muko yanzune zamuyi zaman auren tsaftatacce, takuma nunamin nabi komai a hankali, tasan yayi kuskure amma bata hanyar tonama kanmu asiri zan nuna masa kuskurensa ba, kodan matsalar gidanmu ai saina duba, ni macece inada damar juya komai cikin sauk'i, nama iya zama dashi a lokacinda yake ik'irarin auren yarjejeniya bare kuma yanzu daya furta yana sona da bakinsa. Naji dad'in shawarwarinta, nakuma fahimceta sosai, Naimata godiya kuma, da alk'awarin amfani da shawararta insha ALLAH. Hakama mama Rabi'a tak'aramin nasiha da gargad'i mai yawa akan karsuji karsu gani, Na tsare musu mutuncinsu, Dan kowa da tarbiyyar gidansu yake ado. Itama na amsa mata da insha ALLAH zan kiyaye. A y'an gidanmu kam Maman Fauziyya Ce kawai tamin fad'a, amma sauran babu wadda tace nayi mai k'yau ko mummuna, wannan ba matsalarsu baceba, nima ban damuba, Dan wad'anda suka Isa dani sunmin kuma ya wadatar. yayinda zasu tafi rungume juna mukayi da Siyama da Munubiya, Zarah muna hawaye, jimuke tamkar karmu rabu. Dan wlhy yanzu nikam tausayi suke bani, koma miye dai iyayen su mata da k'addara Ce taja musu. Inaji ina gani suka tafi suka barni da kewa, danma laraba Na nan. Suna wucewa laraba ta kalleni, cikin dabarunsu Na tsoffi tace, “koyaya jikin magajin garin?”. Kaina a k'asa nace, “inaga barci yake iya”. Tayi murmushi, Dan kunyar Munaya da kawaicinta Na burgeta, yanda idon yaran yanzu ke a bud'e da rashin kunya a halinyanzu, da watace tuni tanufi d'akin mijin. tace, “yakamata to kiduba koya tashi, da saiki samu kayan k'amshi ki dafasu, insha ALLAH yasha Na kwana biyu sai murar ta barshi”. Godiya Na mata sannan Na mik'e a kunyace Na fita. A falon dazai sadani da sashensa naci karo da Muftahu, barka da zuwa yakuma yimin muka kuma gaisawa amutunce. Yace, “Boss d'in Na ciki kuwa? Dan sarkin k'ofa yace yayi sallama Dan nemamin iso yaji shiru”. Nace, “Ai bashida lafiyane, maybe ma barci yakeyi, mura ke damunsa, amma bara Na duba ka shigo”. Cikeda tausayawa Muftahu yake fad'in “Kai aikam mura Na wahal dashi sosai Idan ta damk'esa, shiyyasa bayason zuwa Nigeria lokaci irin wannan Na sanyi, aini banga ta shigaba, bara naje muzo da doctor jalal daganan nasamo muku abinda zakuci, yanzu haka yinin yau baici komaiba”. Godiya namasa ya juya ya fita, nikuma na nufi k'ofar falonsa. Tun a falon na tabbatar mai d'akin babu lafiya, Dan komai a kashe yake har AC, Wanda inhar yana gidan AC yini yake yana aiki, koda uake akwai sanyi yanzu, shi ko damunsa bayayi ma, Na k'arasa k'ofar Bedroom d'in, harna kai hannu zanyi knocking kuma saina fasa, tura k'ofar nayi a hankali da sallama Na shiga, d'akin dund'um da duhu gashi bansan ina makunnar fitilar take bama ni, tsaye nayi ina tunanin mafita, na komane ko nayi magan...? Galadima dake kwance yau yini guda cikin halin ciwon kai da zazza6i, salla Ce kawai ke tadashi, abincima da k'yar ya had'a shayi yasha bayan sallar la'asar, tunda ta shigo yana jinta, saidai baisan wanene ba, shi a tunaninsa ma wanine yazo cutar dashi, jin anyi shiru ankuma k'i magana ya mik'a hannunsa da k'yar ya kunna fitilar dake dirowar gefen gadon. Baya nad'anyi kad'an danni tsoratama nayi, harma na fara zaton kobaya d'akin, sai kuma na nutsu waje d'aya ina kallonsa, yana cikin bargo ya lullu6e har kansa, janye bargon dake lullu6e da fuskarsa yayi yana kallona ta cikin d'an hasken fitilar. Idanu ya zuba mata cikeda mamakin yaushe tazo gidan? Ya ciro hannunsa daga bargon yana min alamar nazo. A hankali na cigaba da takawa, zuciyata cike da d'unbin tausayinsa, koba komai ta sanadina ciwon ya sameshi, na zauna a bakin gadon idona a kansa, hannuna ya kamo cikin nasa dakeda zafi alamar zazza6ine ma a jikinsa. Ina had'iye kukan daya tahomin nace, “Sannu, ya jikin?”. Idanunsa ya lumshe da cije lips. Na kama bargon zan yaye yakuma rik'e d'ayan hannun yana girgizamin kai, ahankali yace, “Sanyi”. Sannu na kuma masa, sannan na zare hannuna zan mik'e, amma saiya rik'oni da sauri, jiyowa nai ina kallonsa. Ahankali Yace, “Ina zakije?”. Badan ina kallon la66ansa ba dabama zan fahimci miyace d'inba, Dan banjiba. Dawowa nayi na zauna, nad'an matsa hannunsa, “zan had'a maka ruwane kasamu kad'anyi wanka, kaci abinci kuma”. “Zan daiyi wankan kawai?”. “Abincin fa?”. Kansa ya girgizamin alamar a'a. Kamar zanyi magana saikuma na fasa, tashi nayi na shiga toilet, dukda babu wani datti dai sai naga yakamata na wanke, na cire mayafin jikina na tsaftaceshi, na saka air freshener sannan na had'a masa ruwa mai d'an zafi ba canba dai, yanda zai masa dad'i. Zaune na iskeshi a bakin gadon ya dafe kansa, kallo d'aya namasa na d'auke kai, Dan dagashi sai boxer. “Ga ruwan na had'a”. 'Dago idonsa yay ya kalleni yana sauke hannunsa daya dafe kai, yanda tawani k'asa dakai kamar tana gaban surukinta, yad'an murmusa danshi kunyar nan tata birgeshi take. Duk saina takura da kallon dayakemin, gashi kunyar motsawa nake daga wajen, Dan sket d'in jikina ya kamani sosai, maganarsa Ce ta katsemin tunani. Na d'ago ido naimasa kallon fisha na janye ina fad'in “Towel?”. “Uhumm”. Kawai yace yana cigaba da kallonta. Ahankali na dunga tafiya saikace wata mai tatata, Dan inaji a jikina kallona yakeyi har yanzu, saida na d'akko gyalena dake jikin k'ofar bayi na yafa sannan na d'akko towel d'in. Duk abinda takeyi idosa na kanta, towel d'in da hannunna ya had'a ya rik'e, na kallesa fuska a marairaice ina f'ad'in, “karfa ruwan ya huce yalla6ai”. Ya zubamin jajayen idonsa ga jijiyoyin kansa sunyi rad'a-rad'a, baice komaiba ya zare towel d'in ya yafa a jikinsa yana mik'ewa da k'yar, saiya kuma bani tausayi, Dan na lura k'arfin haline kawai yakeyi. Bedsheets d'in saman gadon Na cire bayan Na kunna fitilar d'akin ya gauraye da haske, Na bud'e wardrobe d'in kayansa Na d'akko wani bedsheets d'in Na shinfid'a, Na share d'akin, banyi morping ba tunda darene, nasaka turare sanann Na fita. Yauce rana ta farko dana shigo kitchen da nufin dafama miji abu, sainakejin karsashi da alfaharin nimafa yanzu matar aurece tamkar kowacce mace, natashi daga matar Contract yanzu, wasu hawayen jin dad'i suka zubomin, nasa bakin mayafin Na share, a kayan da mukazo dasu Na ciri kayan k'amshi, ina d'auraye tukunya laraba ta shigo, juyowa nai ina kallonta. Tace, “ya jikin nashi?”. Ajiyar zuciya nad'an sauke. Nace, “da sauk'i iya, amma kwance Na iskeshi rijib ga zazza6i, zan dafa masa ruwan zafinne da d'an abinda zaici”. “ALLAH ya k'ara sauk'i, dama mura bata masa da sauk'i, dan yasha zuwa can yanayi kota sameshi a can, namiki karambani Na dafa ruwan zafin gashinan”. “Nagode iya, wlhy babu wani karbani, taimako dai, mun saki aiki ga gajiyar tafiya”. Dariya tayi tana gyara tsayuwa. Tace, “Aini gajiyarnan kam ta gudu, ras nakejina, kunedai dayake ba wahalar kuka saniba koyaya kuka motsa sai jiki yayta ciwo”. Nima dariya nad'anyi, ina cigaba da had'a komai akan k'aramin tire. Laraba tace, “To yanzu Yaya za'ayi kenan da abinci? Kinga dai ba'a barshi da yunwa ba?”. Nace, “Iya ga Muftahu can ya tafi samo masa abincin”. Tace, “To shikenan hakanma yayi”. 'Daukar tiren nayi natafi kai masa. Har yanzu bai fitoba, mamakin dad'ewarsa ta kamani, ajiye tiren nayi a k'aramin table glass d'in dake gaban gadon nima Na zauna ina tsumayen fitowarsa. Kusan mintuna 3 da zamana saigashi ya fito. Ban kallesa bama gudun karnaga abinda yafi k'arfina, kaina a k'asa ina wasa da stones d'in jikin mayafina. Shikam tunda ya fito idonsa Na kanta, ya zauna kusa da ita yana tsane ruwan fuskarsa zuwa kai da towel. Kallonsa nayi kad'an, ganin bathrobe ce a jikinsa saina samu nutsuwa. Da hannu yay min nuni da mansa, na mik'e Na d'akko, amma saiyak'i kar6a. Nad'anyi shiru da tunanin miyake nufi?... Katsemin tunani yayi da fad'in “Manma nizam shafa?”. A hankali yayi maganar, kuma fuska babu walwala. Ni mamakima yabani, amma to da banzo ba waye yake shafa masa?, bance komaiba na zauna kusa dashi ina zuba man atafin hannuna da mutsukashi, kunya tasa narasa dama ina zan fara?. Lura da hakan dayayi saiya mik'amin hannu kawai, banida za6in daya wuce cika umarninsa, anutse na shafa masa man dan banida yanda zanyi. Kaya na d'auka masa marasa nauyi, ya tashi zaune daga kwanciyar da yayi ya saka, nidai kauda idona nayi gefe harya gama. Natashi na had'a masa tea d'in da ruwan kayan k'amshinan, yana zaune akan sofa ya zubamin ido saikace wata television, dana mik'a masa mug d'in saiya had'a harda hannuna ya rik'e, da ido namasa alamar da zafifa cikin marairaicewa. Shima saiya min nasa salon da ido alamar da gaske. Nakuma narke fuska tamkar zanyi kuka, zame mug d'in yayi yana wani miskilin murmushi. Ya d'ora cup d'in akan bakinsa yana kallon yanda take tatta6a tafin hannunta, a ransa yace hajiyar tsiwa kenan, andawo koya kuma zamu kwashe?. Tea d'in yamasa dad'i, Dan saiya tuna masa da inno, itace kan masa wannan had'in inhar yana mura, yanasha yana kallona a k'asan ido, saika rantse kuma ba kallon nawa yakeba, amma ni inaji a jikina. Knocking k'ofar da akaine ya sashi kallon cctv, ganin Muftahu da Dr jalal sai ya juyo ya kalleni da alamar tuhuma. Uffan bance da shiba, na mik'e da nufin fita na bud'e musu saiya dakatar dani ta hanyar d'agamin hannu. Komawa nayi na zauna, shikuma ya mik'e rik'e da mug d'in ya fita. Ajiyar zuciya nad'an sauke ina binsa da kallo. Saida ya zauna cikin kujera sannan yabama su Muftahu izinin ahigowa. Duk suka zauna suna masa sannu, ya amsa musu cikin d'aga kai da basu hannu sukayi musabaha. Magunguna Dr jalal ya bashi na mura. Sannan ya buk'aci yimasa allura, amma saiya nuna bayaso. Cikin dafe kai yace, “bar Allurarnan Jalal, bara nasha maganin kawai”. Murmushi Dr jalal yayi, Dan yasan dama Galadima bayason allura. Basu wani dad'eba sukai masa sallama suka fita. Fitarsu dana gani yasani fitowa falon, kallonsa nayi ina zama, shima idonsa a kaina, da hannu ya nunamin ledojin da Muftahu ya ajiye. Bance komaiba na bud'e, d'aukar d'aya nayi na fita, na kaima laraba dakema su Abdurraheem shirin barci. Cikin tsokana tacemin “kodai murufe d'akinmu kawai”. Dariya nayi na fita ina fad'in “kai iya yanzufa zan dawo”. Inajiyo dariyarta daga falo. Nidai nashiga kitchen na d'auki plate da spoon na koma wajensa. Farfesun kifi na zuba masa, dan zaifi masa sauk'in ci, da farko ma cayay bazaiciba, saida naita rok'onsa harda kwalla sannan ya amince nabashi da kaina, yad'anci babu laifi, nabashi drugs d'in da Dr jalal yabashi”. Koda yagama sha saiya jingina jikinsa da kujerar yay shiru, yad'anji dad'in jikinsa kam ba laifi, falon saiya d'auki shiru, muna a hakane kiran Momma ya shigo wayarsa. Yabud'e idanu yana d'aukar wayar, yay picking, gaisawa sukayi, bansan mitace da shiba daga can najidai ya amsa da “Insha ALLAH goben muna hanya”. A hankali yake maganar saboda kansa, bama su dad'eba ya yanke wayar ya mik'e, hannu ya mik'omin alamar na kama. Banyi musuba na saka hannuna cikin nashi ya mik'ar dani, bedroom d'in muka koma, ya zaunar dani bakin gadon sannan ya cire kayan jikinsa, ya hau gadon ya kwanta. Nidai k'in kallonsa nayi, saida ya kwanta sannan ya kirayi sunana a hankali can k'asan mak'oshi, kallonsa nayi. Yace, “Please mammatsamin jikina kozai rage ciwon da yakemin”. Tausayi yabani, dan haka banyi musuba na hau gadon sosai nafara masa tausa a nutse, idonsa ya lumshe yanamai jin dad'in tausar, ahankali drugs d'in dayasha yafara cin k'arfinsa, barci mai nauyi yay a won gaba dashi, saida na tabbatar barcin yayi nisa sannan naja bargon na kuma lullu6a masa har saman kafad'a, nai masa addu'a na mik'e Na lalla6a na fita a d'akin bayan na kashe masa fitila. Koda na koma d'aki laraba har tayi barci, nima shirin kwanciyar nayi kawai na kwanta, cikeda kewar y'an uwana da jiya iyanzu duk muna a tare😔. ******************** Iyayen Su Munaya maza sunyi farin ciki da labarin da Abba yabasu akan dangin inna, dan suna tausayinsu sosai, innaro ta tarasu duka tasa aka kira mata inna, harda hawayenta tana Neman gafararta bisa ga abinda tamata tsawon shekaru. “Kiyafemin Ai'sha, dan lallai son zuciya ya rufe idona ruf, banason ara6i y'ay'ana koni saboda abin duniya, nata k'ask'antar dake agaban wad'anda duk kin rigasu zuwa gidan, wlhy wani lokacin su mero ne suke zugani, dan ALLAH kiyi hak'uri, nasan dai da wuya ki yafemin ma.....”. Da Sauri inna tace, “Wlhy na yafe miki nikam, dama ban ta6a rik'eki a raina ba, dan matsayin uwa mahaifiya nake kallonki, inhar bazan iya musawa mahaifiyata magana ba ko jin zafinta to lallai kema baki cancanci na musa mikiba, ni dukanku ma na yafe muku wlhy, ALLAH ya kare gaba, yakuma yafe mana baki d'aya”. Su Abba duk suna amsa da amin, kowanne yanajin dad'i har cikin ransa, lallai idan kaga halin girma to daga tsatson d'an masu girma ya fito, duk cin kashin da innro tama innarsu Munaya hakan baisa ta gagara yafe mataba, ya rabbi kabamu k'yak'yk'yawar zuciya gaba d'aya. Masu samun fawar cin zarafin inna a wajen innaro duk sai suka nutsu suma, dan yanzu kam babu dama. Haka su inna sukaita rabon tsaraba akaita rabo, har gidajen iyayen su Maman safara'u duk saida aka kai, kafin kacemi labarin tushen inna yabaje anguwa, mutane sai mamaki da al'ajabin hikimar ubangiji sukeyi, lallai Maman biyu tazamema matan gidansu RAINA KAMA, su sunata hura hanci y'ay'an wasune, da mata gorin rashin dangi Ashe gaba da gabanta, aifa matan anguwa suka dinga shigowa mata murna da sannu da zuwa. Matan gidansu Munaya bak'inciki tamkar zai karsu, saidai babu damar koda yin tari, saidai kukan zuci da bak'incikin hassada mai cinye farin cikin Bawa. ****************** Washe gari Galadima yatashi dad'an dama-dama, dan babu zazza6in sai ciwon kai, shima bamai tsananiba irin na jiyaba. Da safen yake sanarmin nayi shiri wai zamu koma, mamaki ya kamani, wannan wace irin tafiyace haka babu shiri, bayanma naji yanata kukan rashin kud'i a tsakaninnan, saidai banida damar Musawa, dan inason zuwa naga jikin Abie nima. Da yake tafiyar saida yamma, tashin hantsi muka shiga cikin gida gaida mutane, fada Ce kawai bamujeba, sai yaran aka kai can, kowa yana yaba k'yawu da girman da yaran suka k'ara, gimbiya zulfa dai bata yarda mun gantaba, wai batada lafiya tana kwance. Bamuce komaiba muka fito, mun iske Galadima yana fada, dan haka muka cigaba da shirye-shiye, sai a waya na kikkira mutane mukayi bankwana, naso had'uwa da Aunty Salamah dan inason ta warwaremin wasu tambayoyi, to amma hakan bata samuba, ko gidansu baba mai k'anwa ban lek'aba, kuma wlhy naso hakan matuk'a, to amma ga ayanda tafiyar tazo babu shiri. K'arfe 2:00 mukabar masarautar gagara badau zuwa masarautar su papi, tarba akai mana ta mutunci, ina mamakin yanda suke matuk'ar k'aunar Galadima, Sauban tamkar zaiyi rawa dan dad'i, ammafa yayi 6ul-6ul dashi alamar yanashan gata, dukda lokacinmu k'urarrene munsha fira, inno tsohuwar mutunci, yanda take jana ajiki abin ba'a magana. Galadima ma tunda suka gaisa da papi da mutane saiya shige cikin d'akin inno ya kwanta, dan bayason yawan hayaniya, saida akayi magrib muka baro masarautar cikeda d'unbin alkairin wad'annan bayin ALLAH, alkairi sosai Galadima yay ma laraba, harda hawayenta nima haka, dan munyi sabo sosai, bansan miyasa Galadima baice mutafi har itaba, kokuwa matsalar kud'ice oho, lallai na yarda sabo Turken wawa, shi akema kuka ba mutuwaba. Nuren ya d'auke mu. Mun biya gidan Mom, itama dai haka tasha hidima damu, saidai akwai yarinyarta ta biyu nakula tun a wancan zuwan bata yina, dan ko gaisheni bama yi takeba, tata yatsine-yatsine kenan, a wancan zuwan abin yad'an dameni, amma yau ko a jikina, dan abinda na lura dashi son Galadima takeyi, dan haka na watsar da lamarinta ko kallo bata isheniba, babu mai takani na zauna, babu ruwana da arzik'inka ko ahalinka, ka mutuntani nima na mutuntaka saimu zauna lafiya. Wanda takeyi donshi d'inma ko kallo bata isheshiba, dan baya sakar musu fuska, duk shakkarsa sukeyi har babban wan nasu gaba d'aya, dan ko sauban ya girmeshi balle Galadima. Bamu bar gidanba saida time d'in tashin jirginmu ya matso, dan tacan zamu wuce, dukansu gidan sukai mana rakkiya har airport, har saida sukaga tashin jirginmu. ************** Abin ya had'emin da yawa kam, ga yara ga babansu daba lafiya, sauk'inama basuda yawan rigima, Abdurraheem ne dai idan yaji ya takura babu zaman lafiya, Alhmdllh ALLAH dai ya taimakemu mun Isa lafiya, Khumar da Samha, aunty Mimi sukazo tararmu, bama tamu sukeba ta yaran sukeyi, ganin haka Galadima yaja hannuna muka shige mota, saida suka gama murnarsu sannan suka shigo, aunty Mimi na fad'in, “Oh shine kuka shige mota?”. Galadima yabata amsa da cewa, “Tunda batamu akeba mizamu zaunayi”. Dariya ta sanya da fad'in “yau naga kishi, to kuma dai sannunku badan halinkuba”. Murmushi nayi ina gaisheta, Samha ta mak'alk'aleni. Haka dai muka k'arasa gida. Momma da jakadiya duk suna a harabar gidan da sauran hadimai mazan da mata. Kowa burinsa yaga yaran. Momma dai Nita rungume tanamin oyoyo. Kunya dukta kamani, ina k'aunar wannan baiwa har cikin raina wlhy. Galadima kam jingina yay da mota kawai yana kallonsu cikeda jin dad'in yanda kowa ke farin cikin dawowar iyalansa. Saida muka shiga ciki sannan Momma kecewa “Ina uban gayyar wai?”. Galadima dake shigowa a k'arshe yace, “gani a anan, naga batani akeba Momma shiyyasa naja gefe”. Duk dariya mukayi, yayinda bayin sukai k'asa da kai duk suna k'umshe tasu, dan babu damar yi. An shiga gaishe-gaishe damana sannu da zuwa, hadiman gidan duk suka fice aka barmu mu kad'ai. Momma duk tana rungume da jikokinta wad'anda suke rikid'ewa ruwa biyu, kamannin Galadima da Munaya, Khaleel ma yabi ya mamuk'e mata. Galadima ya mik'e ya haye sama, danya d'an watsa ruwa, gashima magrib tagabato anan. Momma harda hawayenta najin dad'i da farin ciki. Tofa lamari ya canja salo, a wannan karon dai maimakon Momma tace nabi mijina saitace na shiga d'akinta nayi wanka na huta, aunty Mimi kuma ta kwashi yaran da taimakon Samha zata musu wanka. Nikam hakan yamun dad'i, dan dama banason zama d'aki d'aya dashi. A d'akin Momma nai wanka na canja kayana, ina shirin kwanciya Samha ta shigo kirana wainazo naci abinci. Galadima yay ta zuba idon shigiwar Munaya amma saiyaji bulum. Da farko bai kawo komai a ransaba yashiga toilet danya watsa ruwa, jikinsa babu k'arfi har lokacin, dayake d'akin tsaf yake an gyara ko ina fes yanata k'amshi. Mamaki yakuma kamashi daya fito har sannan babu Munaya babu dalilinta, ko mai bai shafaba ya zura jallabiya ya sakko, Momma na zaune a falo, harya gama sakkowa idonta na kansa, duk sai ya rame mata a ido, ga hancinsa yay jajir alamar mura tamasa ligif, tissue d'in hannunsa ya ajiye sannan ya zauna. Momma tace, “Sannu Muh'd dukka rame, mura na wahalmin da kai wlhy”. Murmushi yad'anyi yana shafa sajensa. Yace, “My Sweet Momma to yaza'ayi, yanzu hakama kaina ciwo yake, ya muka sameku?”. “Lafiya lau, sai kewarku, ya kuka baro manasu da autana?”. “kowa lafiya, Autanki nacan nama inno ta6ara, bakiga yanda yay k'iba ba ma”. Momma tayi dariya tanacewa, “Ja'iri, da yanata zum6ure-zum6ure bazaijeba, bagashi haryaci wata kusan uku ba, kwana nawa zai gama”. “Dama ai shagwa6ace Momma”. Momma tayi murmuahi tana maida kallonta ga jakadiya dake maganar ga abinci. Sannu Tamata, ta kalli Galadima daya jingina da kujera ya lumshe ido. “Muh'd tashi ga abinci ko, kasamu ka kwanta ka huta”. Idonsa ya bud'e yana mik'ewa, saiga Samha da aunty Mimi sun fito suma. momma tace, Samha ta kira Munaya tazo taci abinci. Galadima yanaji amma baice uffanba, saima maida hankalinsa yayi ga abincin da Aunty Mimi ke zuba masa. Ya faracin abincin Samha da Munaya suka fito, kallo d'aya yamusu ya d'auke kansa zuciyarsa na mamakin miya kaita d'akin Momma?. Duk Momma na kula dashi. Itama Munayar kallonsa tad'anyi ta d'auke kai. Haka akaci abincin duk hirar dasu Momma sukeyi da Munaya Galadima baice uffanba, cin abincin sa kawai yakeyi, baima wani ci da yawaba ya matsa gefe alamar ya k'oshi. Aunty Mimi tace, “my K'ani Yaya dai?”. Yad'an yamutse fuska da fad'in “Alhmdllh ya isheni”. “Ai kai dama tsiyar murarka kenan wlhy Sameer, ta jigataka ta hanaka cin abinci, ALLAH ya kara sauk'i”. Cikin lumshe ido ya amsa da amin a saman la66a. Muma duk sannu mukai masa, ya d'aga mana kai kawai. Koda muka had'a ido saiya zubamin wata harar gargad'i, murmushi nayi na kauda kaina gefe tamkar ban ganiba.....................✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣6⃣ .................Momma dai ta kasa ta tsare ta hanani hawa sama, idan abu Galadima ke buk'ata saitace Samha ta kai masa, tsakanina dashi saiya sakko gaidasu ko zaije massalaci, ya kumak'i nuna hakan ya damesa, sosai mamaki ya kamani, dan kwanakinmu hud'u kenan da dawowa, da farko na d'auka kawai shariyar tasa ta k'asaitace ta motsa, amma zuwa yau dayake shirin zuwa Kashmir sai abin yafara bani tsoro, dan ina zaune bakin gadon Momma ina shayar da Abdurraheem ya shigo, Momma ta fita kitchen. 'Dago ido nayi ina amsa masa sallamar da yayi, amma saiya d'auke kai tamkarma bai ganniba, ya k'araso kusa dani ya rissina ya d'auki Amaturrahman dake kwance tana motse-motse. Duk'owar dayay saitasa k'amshin turarensa bugomin a hanci sosai, na lumshe idanuna sannan na bud'e akansa, magana yake ma Amaturrahman ahankali cikeda k'asaitarnan tasa, saikace wata babba. Da kamar nima zan shareshi, saidai na daure nace, “Ina kwana”. “Lafiya”. Ya amsa batareda ya kalli inda nakeba. Hakan yamin ciwo a rai, na dangwarar da Abdurraheem d'in akan gado batareda ya k'oshiba, aiko saiya saka kuka, banbi takansaba na shige bathroom abuna. Da kallo Galadima ya bita cikeda takaici harta shige, ya cije lips nashi tamkar zai huda da hak'ori, idanunnan harsun kad'a da 6acin rai. Yana k'ok'arin tashi ya d'aukeshi Momma ta shigo d'auke da k'aramin Kofi ma Magani daza'a basu. K'arasowa tai dad'an hanzari tana fad'in “shikuma wannan mi akai masa?”. Ita bama ta lura da Galadima ba, amma taji k'amshin turarensa. Kwafar da yayi yasaka Momma juyowa ta kallesa bayan ta d'auki Abdurraheem d'in. “Wai dama kana d'akin amma yake kuka? Ina Munayar ne?”. Baice komaiba sai bayi ya nuna mata da hannu, hakan yasata fahimtar ransa a 6ace yake, ta zauna tana shafa bayan yaron, yayinda shikuma ya daina kukan. A kausashe Galadima yace, “Momma idan bazata iyaba na nemo masu kulamarmin da yara, dan bazan d'auki wannan wulak'ancinba, ta k'auracemin na k'yaleta tayi duk yanda ta gadama, shine yanzu kuma abin akan yarana zai dawo, nifa wlhy......” Dakatar dashi Momma tai ta hanyar d'aga masa hannu, “ya Isa haka Muh'd, Munaya dai matarkace, kuma lafiyar ALLAH kuka dawo k'asarnan, aganina tun washe garin dawowarku kaga batazo inda kakeba yakamata ka tambayeta miye dalili? Amma ka share tamkarma hakan bai damekaba, shin mulki haukane Muh'd? Indai kace zakaima mace izza da mulki wlhy kana tare da wahala, dan ba kowace mace bace zata d'auka, gaka da zuciyar tsiya saikace kuturu, ni nasan minene matsalarkune balle na sasantaku? Kuka Sani, inma zaku shekara a hakane kuyita zama babu ruwana wlhy”. Shiru Galadima yay yakasa magana, zuciyarsa sai zafi take masa. Momma kam ta d'auki Abdurraheem da maganinsu tayi ficewarta tabar musu d'akin, sumaci Kansu ita babu ruwanta. Kansa ya dafe cike da takaici, shi yarasa gane kan Munaya, da farko yabartane yaga iya gudun ruwanta, a tunaninsa ko kunyace, amma daga baya saiya fahimci ba haka bane, wani tsirin ne kawai take Neman k'irk'ira, kud'i ya ajiye mata shima ya fice d'auke da y'arsa a kafad'a. Munaya dake a bayi tana kuka ta wanke fuskarta ta fito danjin alamun ya fita. Kwanciya tayi saman gadon wasu hawayen na zirarowa, itafa koma mizaiyi tana akan bakanta, dolene saiya kar6a laifinsa sannan koda zai sameta yanda yakeso. A can falo Samha yabama Amaturrahman yay musu sallama ya fita. Shareshi momma tayi, sai aunty Mimi ce tace, “Dan ALLAH Momma Ku tsaida shirinan naku keda mom, kubashi matarshi, yanzune hankalinsa ya kwanta yadace yasami cikakkiyar nutsuwa da iyalinsa, amma kunbi kun kankane, haba dan ALLAH Momma ”. Da 6acin rai Momma ta kalli Aunty Mimi, “To mai d'an uwa, yanzu ke idan Sauban ne a matsayin Munaya zakiso wani yazo ya auresa a sigar da d'an uwan naki yayi? Miyasa kukeda son kanku, wlhy kinji na rantse inhar bai gane kuskurensa ya nemi yafiyartaba ta yafe masa bazan ta6a bashi itaba, idan yagadama ya cika gidannan da fushi, kuma aiga y'ay'ankunan mata kun haifa, ba kuma zakuso a aikata hakan agaresuba ince?”. Aunty Mimi ta tausasa murya ganin ran Momma ya 6aci, “tokiyi hak'uri Momma, ni aganina a zaunar dashi a karanta masa laifinsa, kinga shi yanzu dukma baisan dalilinkuba wlhy”. Banza Momma Tamata, ta ajiye Abdurraheem ta tashi takoma d'akinta. Binta kawai da kallo aunty Mimi tayi, tasan akan gaskiya su Momma suke, to amma sai a tausayama Sameer ai shima, akuma sanar dashi laifinsa, tasan halin Momma akan son kwatarma mai gaskiya gaskiyarsa, bakuma zata ta6a tank'waruwa ta sauk'iba, balle ga mom a gefe na angizata. **************** Ran Galadima a 6ace yay wannan tafiya, sauk'inma da yaje yaga jikin Abie ne sai nutsuwa ta saukar masa, har yanzu yanata samun kulawa ta musamman, bakuma a shiga inda yake, amma kullum Dr Erfan cikin ma Galadima albishir yake akan cigaban da ake samu, yauma sosai ya labarta masa komai gameda ga66an Abie da ayanzu zasu iya fara aiki, zasu barsane yad'an k'ara kwanaki domin k'arfin jikinsa da abinda ba'a rasaba, dama ciwo shike shiga lokaci d'aya, amma sauk'i sai a hankali. Kwanan Galadima biyu yadawo new Delhi. Ranar kamar wasa Munaya da Samha suka shiga kitchen wai zata koya mata tuwo, har Momma na musu dariya da tsokanarsu yau zasuci tuwon y'an gayu. Daga abin wasa sai Munaya ta zage tayi nutsetstsen tuwo da miyar ganye, tamusu juns na kayan itatuwa, gamawarsu kenan sukaje zasuyi wanka, Momma da Aunty Mimi na zaune afalo suna jiran suyi wankan azo abasu tuwo suci, su Abdurrahman duk suna tare dasu aunty Mimi na yanke musu k'unba, Yayinda jakadiya ke tayata, babu Wanda ya sanarma zaizo, sai kawai sukaga ya shigosa da sallamar nan tasa ciki-ciki. Duk juyowa sukai suna kallonsa da mamaki, jakadiya ce kawai tasami damar amsa masa, sai Khaleel dake wasa ya tafi da gudu yana masa oyoyo. 'Daukar yaron yay ya d'aga sama, dukda yayi girma masha ALLAH. Ya k'araso cikin falon Jakadiya na gaisheshi, amsa mata yayi da kulawa, sannan ya zauna a kujera yana rik'e da hannun Khaleel. Momma tace, “wai dama kana tafe?”. “Wlhy kuwa Momma”. Yafad'a cikin sauke numfashi, itama ya gaisheta. Itama aunty Mimi suka gaisa, tana masa sannu da tambayarsa jikin Abie. Cikin fad'in “Alhmdllh” ya amsa musu, yabasu labarin cigaban da aka samu, farin ciki na manaye zukatansu. Ajiye ruwan da baiwar tamasa yay dai-dai da fitowar Munaya cikin matsakaiciyar kwalliyar data k'ara mata kwarjini da cikar haiba, dan zani da rigane na atanfa, ta fito asalin bahaushiyarta jinin buzaye tawani fannin. Lokaci d'aya idonsa ya sark'e cikin na juna, kowanne sirrikan kewar d'an uwansa na fita daga cikin nasa, Munaya tafara d'auke kanta, yayinda shima Galadima ya janye nasa cikeda basarwa. Jitai tamkar karta k'araso, amma kowa yarigada yaganta, tadai k'araso tana masa sannu da zuwa. Amsawa yay cikin halin ko in kula. Ita Momma dariyama suka bata, hakama aunty Mimi data maidasu television. Ajiye Abdurraheem d'in yayi yatashi wai zaije ya watsa ruwa. Munaya tabisa da kallo a sace, sanye yake cikin k'ananun kaya, wando ruwan toka da farar riga mai d'ishi-d'ishin ruwan goro. Tad'anyi 6oyayyar ajiyar zuciya tana kauda idonta lokacin daya juyo, dan jiyay a jikina kallonsa akeyi, aiko saigashi ya kama yalla6iyarsa dumu-dumu. Baki yata6e ya ida hayewa yana sak'ama zuciyarsa matakin daya shirya d'auka akanta. ******** Ba'a zauna zaman cin tuwonba saida Galadima yay wanka ya sakko, duk suka hallara wajen cin abincin, Momma tama Munaya nuni da ido tayi saving nashi. Babu musu tabi Umarnin Momma, yanata latsa waya tamkarma baisan hidimar da sukeba, ga fuska cinkus babu walwala, dukda zuciyarsa na kwad'ayin fara cin abincin da k'amshin ya addabi hancinsa tun d'azun. Tana gamawa takoma mazauninta da Samha ta shiga tsakkiyarsu, ya ajiye wayar yana kuma wani d'aure fuska dacin Magani, yayi mamakin ganin tuwo, dukda dai Dama akanyi musu amma sai time to time, shiyyasa yake sonsa sosai. Hannunsa ya wanke a ruwan da aka ajiye masa, baici da tsokalin data ajiyeba. Tun a laumar farko kunnensa ya nemi tainkewa, 100% yaji yakamata ya baima mai wannan girkin maki. Momma da Aunty Mimi dai kam kasa hak'uri sukayi, suka shiga santi da yaba wannan tuwo, Galadima dai yayi tsitt, sai a zuciyarsa yake yabawa, cikeda tsokana Momma tace, “wasuma dai santin nasu na shirune, suna tsoron yin magana dad'in ya yanke”. Dariya su aunty Mimi sukayi, Munaya ta saka d'ankwali ta kare bakinta tana murmushi, dan kowa yasan dashi Momma take. Galadima da yasan dashi Momma take shima saiya murmusa yana satar kallon Munaya. Saida suka gama tsaf Momma ke cewa lallai d'iyata sannu da k'ok'ari, rabon danaci tuwo irin wannan mai dad'i tunna inno, har k'yauta yau saina miki”. A kunyace Munaya tace, “godiya nake Momma”. Dukda Galadima ya fahimci girkin Munaya tayishi baice k'alaba, saima ya d'auki waya yay kira, ya mik'e ya fice harabar gidan. Aifa nan suka shiga gulmarsa suna dariya, Samha harda cewa tana ganinsa yana lumshe ido lokacin fayakecin tuwo. Aiko mizasuyi inna dariyaba. Koda yagama wayar bai koma cikin gidanba, saiyay ficewarsa saboda gabatowar lokacin salla. *_9:30pm_* Galadima ya sakko daga samansa, fuskarsa kawai zaka kalla kafahimci yana tare da damuwa, sanye yake da kayan barci farare sol, wandon yaje har k'waurinsa amma baikai k'asaba, sai k'amshi mai sanyi yakeyi. Cikin sand'a ya tura k'ofar Momma yad'an lek'a kansa, Munaya kad'ai ya hango zaune abakin gado tana tofama yaran addu'a a tafin hannunsu tana shafa musu a jiki, ya kalli ko ina babu alamar Momma saiya ida shigewa. Shigowar Mutum kawai Munaya ta gani, tsorata tayi, ta kware baki zatayi ihu yay azamar saka tattausan hannunsa ya toshe bakin, k'amshin turarensa ya sakata fahimtar shine, d'aukarta yay gaba d'ayanta tanata mutsu-mutsu da k'afafu dason yin magana amma babu dama. Yanufi k'ofa da ita zai fice Momma ta fito daga bayi, daga bayansa kawai yaji ance, “Sannu shugaban masu iya satar mutane, to saika ajiyeta ai”. Fad'uwar gaba da kunya dukta lullu6eshi a lokaci d'aya, ya dire Munaya yana susar k'eya saboda kunya, yama kasa kallon Momma d'in. Itakam bata kuma cewa dashi komaiba tazo ta gabansa ta fita d'akko abu. Yana ganin Momma ta fita saiya juyo ga Munaya da hanzari. A matuk'ar fusace yay kanta, “K! y'ar rainin hankali ALLAH yau saikin sanarmin minayi miki, inba hakaba a d'akinan zan kwana, bar ganin Momma ta tsaya miki”. Ja da baya Munaya tayi ganin yana Neman maketa, idonta cike da kwalla tace, “Ai kaima kasani”. Hannu ya d'aga tamkar zai maketa saikuma ya fasa, ya dunk'ule hannun, “ke wai wace irin mutumce birkitacciya?, ba'a ta6a zama dake lafiyar ALLAH?, kinsan ALLAH wannan karan Abban zan kira Na sanarmawa idanni kin rainani.......” Cikin kuka munaya ta katseshi, “Dama kasanar masa ai shine ya kamata, kaga shima zaisan tayaya ka aurar masa yarinya, Papi da mai martaba zasusan Neman auren shekara biyu sukaje suka nema kuma suka d'aura.....” Kansa ya dafe cikin tsantsar takaici, miye kuma nadawo da wannan maganar bayan ta wuce? Kai yarinyarnan y'ar matsalace. Duk a zuciyarsa yake zancen. Momma da dama duk cikin shirinsune ta fita tai saurin shigowa tana fad'in “Minakeji haka? Waye yayi auren shekara biyu?”. Duk kasa magana sukayi, munaya Na kuka shiko kunya da nadama dukta rufeshi. “Waishin bakujini baneba?!”. Momma tayi maganar a tsawace. “Momma please cool down”. “Nayi cool down a ina Muh'd, dama abinda ka aikata kenan bamu saniba? Yanzu nan da hankalinka da iliminka Na addini da tarbiyyar da muka baka zakaje kayi auren yarjejeniya da d'iyar mutane? Shekara biyu ta cika kasaketa saboda son zuciya? Wannan d'abi'ar daga ina kuma ka samota? Danba koyarwar addininmu bace balle al'adarmu”. Jiki a sanyaye Galadima ya zauna a bakin gadon kansa a dafe, itama Momma saita zauna tana kiran Munaya data mak'ure jikin bango tana kuka maiban tausayi. Takowa tayi tazo inda take, saita zauna a k'asa kusada ita. Momma ta kallesu dukansu, saima suka bata tausayi, Dan takula kowannensu yakamu dason d'an uwansa Na gaskiya, tad'anyi gyaran murya tana fad'in “Muh'd!”. Kallonta yayi idonsa ya kad'a zuwa jaa kad'an, jijiyoyin kansa da gashin jikinsa duksun mik'e saboda damuwa, sai faman cizar lips yakeyi. Momma datasan bazaiyi magana ba tunda yahau sama saita cigaba da maganarta, “Muh'd ka fad'amin gaskiya ya akayi ka auri Munaya?”. Kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru yana kallon Munayar da kanta ke a duk'e tana kuka har yanzu..... “Ba kallonta nace kayiba, amsar tambayata nake buk'ata”. Zamansa ya gyara a sanyaye yace, “Momma ku gafarceni, dama nasan duk daren dad'ewa wannan ranar saitazo, nasan nayi kuskuren aikata abinda Addinina bai koyar daniba, hakama al'adata idan taji zata k'yamaci hakan, saidai wlhy a wancan lokacin banida za6in daya wuce hakan, ban ta6a tunanin son wataba, damuwar mahaifina da ciwonsane kawai agabana, banta6a kallon mace dawata siga ta soyyayaba balle tunanin aure, dukda fad'a da kukemin akan nayi aure a kullum. Bayan jaridar nan ta fita saina shiga rud'ani da zargin an aikotane dama gareni, wannan daliline yasani tunani sakawa a satomin ita Na ajiyeta harsai ta sanarmin wanene ya sata, amma sai Muftahu ya nunamin Sam hakan ba mafita baneba, dama kawai Na aureta, maganarsa ta sakani d'aukarsa mahaukaci, Dan haka namasa gargad'in karma ya kuma yinta, nidai kawai a d'akkomin ita Na tuhumeta. Shikuma yace Sam bazai bani goyon baya bisaga wannan gangancinba, k'yalesa nayi da nufin zan nemo Wanda zaimin aikin. Saidai kuma Nureddin kawai gareni, shikuma a time d'in yana Italy. Kwatsam sai wani tunani yazomin a zuciya da gamsuwa da shawarar Muftahu, Dan gaskiya yafad'amin, inhar wani yasan tana hannuna duniya zata d'auka abinda yafaru a jaridar nan gaskiyane Na aikata d'in, amma idan aurenta nayi bakin kowa zai mutu, inada kuma ikon sata tayi komai takuma sanarmin Wanda ya sata. Wannan ne dalilin dayasani bincike akanta, har nasamu aka d'akkomin ita Na sanar mata buk'atata. Da farko k'in abincewa tayi, amma daga baya bansan dalilinta Na amincewarba. Wlhy Momma kinji Na rantse ban aureta dannaci zarafinta ba, kuma harga ALLAH banso kutse cikin mutuncintaba, wlhy Muftahu ne ya zuba mana pills a hollandia muka sha, ALLAH kuma ya k'addara zuwan yarannan ta wannan silar, tundaga randa Na aikata mata abinda babushi acikin yarjejeniyarmu nayi nadama, nakuma gane kuskurena, tunkuma a lokacin nafara tausayinta, tsakanina da ALLAH badan Na amfanu da itaba Na aureta, saidai nasan koda fad'a mata nayi bazata aminceba, zata d'auka bisa wancan dalilinne nace ina sonta, amma nasha nuna mata inason nata, saita dunga sharewa, bansaniba ta fahimcenine kokuwa bata fahimtaba, wlhy Momma tsakanina da ALLAH nakeso Munaya, kuma nayi nadamar aikata abinda Na aikata, na tabbatar bazanma ALLAH wayoba, ikonsane ya aikata yanda yaso a lokacin dayaso d'in”. Momma tayi murmushinsu na manya tana kallon Munaya, “Na fahimceka Muh'd, amma adalci d'aya zan maka bisaga wannan gangancin naka, adalcin kuwa shine ka saki Munaya a warware auren Contract, saika koma ka kuma Neman aurenta na gaskiya ga iyayenta, ka kuma sanar musu mika aikata musu a farko, kanemi afuwarsu, shima takawa da mai martaba kaje ka sanar musu abinda ka aikata, nikuma namaka alk'awarin zan tsaya maka wajen ganin dawowar Munaya gareka”. Kasak'e yay yana kallon Momma da wannan tsarin nata, toshi mahaukacine dazaiyi wannan gangancin? Ai kowane irin hukunci zai d'auka amma banda na saki wlhy. “wai kobaka jini bane?”. Momma ta katse masa tunani. Narke mata fuska yayi tamkar zaiyi kuka, “Haba Momma Dan ALLAH, yanzunan dakanki kike fad'ar haka? Nidai kimin dukkan hukunci dakikeso amma wlhy banda na saki, bazan iya aikata wannan gangancinba, nayi kuskuren farko amma na biyu kam yana dai-dai daku rasani baki d'aya, wlhy inason matata ina k'aunarta har cikin raina, ni na amince zanje nasami su Abba da papi na sanar musu, nakuma nemi afuwarsu amma banda maganar saki please ”. Shiru Momma tayi tak'i tanka masa, saikuma yabama Munaya tausayi, ita dama burinta ya amince yayi kuskurenne. Haka yaytama Momma magiya amma tak'i tanka masa, shikuma ya nace. Saida Momma ta tabbatar yayi ligif sannan tace, “To ga adalci na biyu tunda ka nace, idan Munaya ta amince ni banida matsala ai, nabaka minti goma kacal zanje na dawo”. Tashi Momma tayi ta fita tana gumtse dariya, saida ta fita tayita sosai, dama akwai randa Muh'd d'inta zai risina irin haka akan mace, Muh'd dazai aikata laifi bada hak'uri ya gagaresa koma yafi Wanda yayma laifin zuciya da fusata, itakam babu abinda zatace da ALLAH sai godiya, Munaya tagama mata komai data zama sanadin canjawar yaronta mai masifar tauri da tsauri. A d'aki kam Momma na fita Galadima ya sakko k'asa wajen Munaya, matsawa tayi baya, ya bita, takuma matsawa, yasake binta, sai kawai ta saka masa sabon kuka. Kansa ya dafe yana fad'in “O ALLAH, Munaya please and Please kiyi hak'uri, nasan nimai laifine amma ki gafarceni, wlhy tun kwananki biyar kacal dakikayi a gidana nayi nadamar aurenki ta sigar yarjejeniya”. Cikin kuka Munaya tace, “saboda kashiga mutuncina ba”. Huci Galadima ya furzar, “Haba Munaya yakike fad'ar haka? Ke shaidace dagani har ke babu mai nutsuwar banbance wani Abu a waccan ranar, sai wahaltuwa da mukayi muduka, wlhy kinji namiki rantsuwa badan na lashi zumarkiba nafara sonki, a lokacin nadamar auren contract da mukayi nayi, amma soyayyarki tafara tsiro da yad'one a zuciyata tamar yanda tushiyar bishiya keyi, wasu k'yawawan halayyarkine suka jani a k'aunarki, rashin tsoronki da d'aukar raini, dukda kasantuwata a gidan dana fito baki amince na takaki yanda nasoba, hakan ya tabbatar min bak'ya cikin mata masu kwad'ayi dason wani Dan d'aukakarsa ko dukiyarsa, yawan ibadarki ya tabbatar min da tarbiyyarki, babbar mallakata da kikayi shine damuwa da ciwon mahaifina, wannan Ce babbar hanyar dakika cusan k'aunarki cikin sauk'i, Munaya kin bada gudunmawa a arayuwata wadda bazan ta6a mantawa da itaba, aduk lokacin da raina ya 6aci kafin shigowarki rayuwata nakan azabtu da motsawar ciwona, na fita hayyacina, bana sauraren kowa sai damuwata, amma kece kika canja wannan matsalar tawa ta k'yak'yk'yawar siga, cikin hikimarki da ilimin da ALLAH yabaki, da kasancewarki mai tarbiya, Dan kowanne tsuntsu da gaske kukan gidansu yakeyi, nasha gwadaki akan abubuwa daban-daban amma kina cinye wannan gwajin nawa saboda zuciyarki a tsarkake take, please ina rok'onki a karon farko ki yafemin, kiyi hak'uri kiyi hak'uri kiyi hak'uri, nimai laifine amma mai nadama, tabbas zanji ciwon wani ya k'ulla alak'ar aure da Samha ma ba Amaturrahman ba ta sigar dana k'ulla dake, amma wlhy inhar kince naje gabansu Abba na sanar dasu komai zanje, nidai karki bari aurenmu ya girgiza koda da igiya d'ayane, namiki alk'awarin samuna fiyema da yanda kike tsammani matata”. Idanu Munaya ta d'ago tana kallonsa, ya jinjina mata kai da lumshe idanu alamar tabbatarwa. Batace komaiba ta maida kanta k'asa. Hanunta ya saka anashi yana matsawa, a marairaice yace, “Kokinason Muhammad Sameer yamiki kukane Munaya? Sannan ki yarda nayi nadama? Wlhy nayi nadama da gaske”. Jikinsa kawai ta fad'a takuma sanya masa wani kukan, shima ya rungumeta yana sakin wasu mugayen ajiyar zuciya, jiyake kamarma ya had'iyeta gaba d'aya ya huta, suzama abu guda d'aya kawai. Momma dake bayansu tashiga tafi tana takowa cikin d'akin. Da sauri Munaya tabar jikinsa tana 6oye fuska, shikansa Galadima yaji kunya, yay k'asa da ido tana murmushi. Momma ta zauna tana fad'in “Alhmdllh ya Ubangijin talikai na gode maka, ALLAH ka d'orar da wannan zama har'a aljanna”. A saman la66a Galadima ya amsa da amin. Munaya dai kunya ta hanata kallon kowa. Momma tace, “Nima yau zan sanar muku abinda baku saniba”. Daga Galadima har Munaya kallonta duk sukayi. Ta gyara zamanta tana murmushi. Tace, “Tun farkon Aurenku nasan komai”. Da mamaki duk suka kalli juna sannan suka maida kallonsu ga Momma. Murmusawa takumayi, “Lokacin da Muh'd ya yarda zai auri Munaya amatsayin auren contract Muftahu ya sameni ya sanarmin komai, danshi burinsa Muh'd ya Auri Munaya ne aure na gaskiya tamkar kowa, a lokacin kuma yasan cewar Gimbiya Zulfa itace ta saka aka muku wannan 6atancin, domin 6atama Muh'd suna, abinda yasa Munaya ta shiga matsalar ranar da kuka had'u a filin idine, shikuma Erfan dayazo miki da suna Fu'ad an sakashi sakama Muh'd idone, saikuma ya ganku tare, duk zatonsa akwai alak'a a tsakaninku shiyyasa yayta bibiyar lamarinki harya kaiku plaza, saidai kuma ya rikice yagaza banbanceku lokacin daya fahimci sewar Ku y'an biyune, shi Muftahu a lokacin bazai iya tunkarar Muh'd da ainahin gaskiyar abinda ya saniba gameda Gimbiya Zulfa da Harun, shiyyasa yayta cusamasa ak'idar aurenki a zuciyarsa, Dan aganinsa hakan zai girgiza zuciyarsu gimbiya zulfa, maybe su aikata abinda Muh'd zai iya farga dasu, ammashi sai rashin yardarsa ta tsiya ta hanashi aminta dake kanki. Gudun karta kwa6e agaba yasaka Muftahu zuwa ya sanarmin komai, yakuma fad'amin nagartarki data ahalinki, ya tabbatar min sai kowa yayi alfahari dake acikin masarautarnan, dansu suna ganin idan Muh'd ya auri y'ar talaka zai k'ask'anta bazaiyi sarauta ba, sun manta ALLAH shine mai komai da kowa. Muh'd yanada tausayi sosai Na tabbata inhar wani Abu ya shiga tsakaninku bazai ta6a sakinki ba, wannan dalilin ya sakani bama Muftahu pills ya saka muku, Dan ta wannan hanyar ne kawai zaku iya zama Abu guda”. Munaya da Galadima duk suka kalli Momma da mamaki, saikuma sukayi k'asa da kai saboda kunya. Murmushi Momma tayi. Tace, “Yes nice nabashi danna kafeku a waje d'aya, nakuma san Munaya zata iya bore akan ka saketa, shiyyasa a washe garin faruwar abin nasaka ka tilas ku taho nan, wannan shine mataki na biyu, mataki na uku saka Munaya tak'i kwantar maka dakai dannasan halinka da bak'in rashin yarda Muh'd, wannan na kula itakuma bata d'aukar saita kwana, shiyyasa abin yamin dai-dai, nadad'e da fahimtar son dakake mata, amma na shareka harsai ka gano dakanka ka fad'a mata. Cikin Munaya shine babbar ribar danaci, wadda nakema ALLAH godiya akowace dak'ik'a ta rayuwata, nake kuma jin k'aunarta har cikin jinina, badan na rabaku na rik'e Munaya ba, nayine dama danna tabbatar da nadamarka, itama ta kuma tabbatar da lallai da gaske kana k'aunarta, ta daina kokwanto a ranta, ALLAH yayi muku albarka, ya k'ara baku zaman lafiya da zuri'a d'ayyiba, yabama Sauban mace tagari shima irin Munaya, itama Haneefa yabata miji nagari kamar mijinta daya bar duniya koma Wanda ya fishi, jikata Samha itama ALLAH yabata miji nagari Wanda zai rik'e mana ita”. Atare muka amsa da amin. Galadima zaiyi magana Momma tace, “kaga d'auka matarka ku tafi dare yayi, da safe ma k'arasa, nikam barci nakeji”. Kunya ta kama Galadima da Munaya, amma Momma saitayi tamkar batasan sunaiba. Tamkar munafukai haka suka mik'e sum-sum suka fice a d'akin, yanda basuyi yink'urin d'aukar yaro ko d'ayaba haka Momma bata tuna musuba itama🤣👍🏻...................✍🏻 *_Masoyan Raina kama amin afuwa dajina shiru, wlhy abubuwane sukaimin yawa, amma Alhmdllh yanzu nafara daidaita, kuma zanyi k'ok'arin gamawa nan kusa da izinin ALLAH, ina muku barka da salla baki d'aya, inakuma jiran naman layya😅🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀._* _wad'anda suka tura hoto kuma Na yafe muku wlhy har zuciyata, wancan write up nayisane lokacin raina a matuk'ar 6ace, yanzu kuma Na huce😅, nayi HAK'URI bisa koyarwar manzon ALLAH, Maman Haneefa ngd kema sosai ALLAH yabar zuminci, yakuma yafe mana baki d'aya, dama raina ya 6acine saboda bansan iya inda hotunan zasu kaiba, idan wani ya gani da k'yak'yk'yawar zuciya wani zai iya munanani ta mummunar hanyar dabanjiba ban ganiba, duk mace tagari bazataso pictures nata suke yawo a social media ba, musamman ma mai aure, kobaka da aure mace darajane da ita, saikuma mutunta kanka ALLAH zai kareka, masu ganin Abu kuna yad'awa jikinku Na rawa kubari wlhy, kokad'an hakan bashida k'yau, Dan kuma bazakuso hakanba, ALLAH ya k'ara mana hak'uri baki d'aya._👏🏻😘😘 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣8⃣ ............A yanda Na kula har yanzu bayajin dad'in jikinsa, dan komai a d'an wahalce yakeyinsa, koda ya fiddo kayan daga wardrobe saiya dawo bakin gadon ya zauna ya dafe Kansa, kallonsa nayi cikin damuwa nima, Na cire Abdurraheem Na kwantar, sannan Na mik'e zuwa garesa, durk'usawa nayi Na d'ora hannayena akan gwiwarsa, “yalla6ai lafiya?”. Shiru yamin kusan minti 1, harna fidda ran samun amsa ma na yunk'ura na mik'e da nufin barin masa d'akinma duka. Hannuna ya rik'o, na juyo na kallesa, har yanzu yana yanda yake baiko d'ago motsa ba. Na cije lips ina had'iye kukan dakeson zubomin, rayuwar nan tasa bana sonta wlhy, ni y'ar dangi Ce, nariga natashi gidan yawa, dukda gidanmu bahagon gidane mukanyi hira koyayane, amma shifa magana ma idan bai ra'ayiba wahala take masa, Abu na damunsa a rai amma bazai iya fiddashi yaji sauk'iba, Momma ta had'ani da aiki, a watannin baya kad'an kamar yafara canjawa, amma gashi yakuma birkicewa yanzu, tayaya Momma take tunanin zan iya canja Galadima? murd'ad'd'en mutumne shi mai wahalar sha'ani, ga tsantsar mulki da k'asaita da suka zama jinin jikinsa, s......... Tunanina ya katse lokacin danaji an jawoni, nai firgigit saboda fad'awa danayi jikinsa, shikuma yay baya ya fad'a kan gadon, kad'an ya rage mu danne Amaturrahman, yad'an kauce kad'an yana sauke ajiyar zuciya. Uffan bai ceminba ya maida idonsa ya lumshe. Mamakin wannan lamari ya kamani, hannu yasaka ya kwantar da kaina a k'irjinsa yana d'an buga bayana da d'ayan hannun, zanyi magana ya d'ora yatsunsa hannunsa uku na tsakkiya akan bakin alamar nayi shiru. banida za6in daya wuce yin shirun, nabisa yanda yakeso. Yanayin da zuciyarsa ke bugawa sai yabani tsoro, na saka hannuna na danne wajen sannan na d'ora kaina bisa hannun, ajiyar zuciya yayi yana cizar lips.. Tsawon mintuna 3 muna a haka, har knocking d'in k'ofa akayi amma baiko motsaba bai barni na motsaba, na yunk'ura zan tashi ya maidani. Munkai mintuna 7 sannan ya zameni ya kwantar ya mik'e zaune, batareda ya kalleni ba ya sauka daga gadon, bathroom ya Shiga, babu dad'ewa ya fito, nidai kallonsa kawai nake da mamaki, Dan fuskarnan amatuk'ar d'aure take tamkar baisan minene dariyaba a rayuwarsa, ya shinfid'a abin salla, domin rama sallolin da suka riskesa yana barci. 6oyayyar ajiyar zuciya na sauke, na tashi zaune idona akan yaran, duk sun koma barci, na tsurama Abdurraheem ido, saboda fitar numfashinsa ta banbanta dana y'an uwansa, tunani nai ko yanayin nasa barcin kenan shikuma, saboda wahalar da suka sha, d'aukar ledar kayan da mom ta kawo nayi, na fiddasu na saka, ban jira ya idarba na fice abina. Nayi mamakin da yanzu babu kowa, harsu Munubiya sun tafi, haushi ya kamani kamar zanyi kuka, aidai sa jira na fito mu gaisa ko? hawayen da suka zubomin a kumatu na share, namafi jin haushin Munubiya wlhy. Sallamar da akeyi na amsa da k'yar, sannan na bada izinin shigowa, cikin bayina ne guda biyu, zubewa k'asa sukayi suna gaisheni. Cikin girmamawa d'aya tace, “dama ance mu gani idan kin fitone”. Nace, “Hummm”. Fahinmatar iya amsar dazan iya basu kenan ya sakasu mik'ewa suka fita, zamewa nai na kwanta cikin kujerar ina cigaba da zirar da hawaye. Kusan mintuna 5 saiga Samha ta shigo, ta durk'usa gaban kujera tana sharemin hawayena, d'ago ido nayi na kalleta, namata murmushin k'arfin hali ina tashi zaune. Muryarta da alamun tasha kuka itama tace, “Aunty Uncle Sam na kiranki”. Kai na jinjina mata kawai, na tashi gaba d'aya na d'auki mayafi muka tafi tare. Koda mukaje k'ofar falon bata Shigaba, nikad'ai na Shiga ita kuma ta juya ta fice daga sashen gaba d'aya. A falo na iskeshi cikin doguwar kujera a kwance, ya kifa yaron d'aya a k'irjinsa Wanda nake k'yautata zaton Abdurraheem ne, wayace manne a kunnensa, amma a hankali yake magana koni danake tsaye cikin falon banaji, na kalli abincin da aka jere a tsakar falon ina zama a kujera. Bai dad'eba ya kammala wayar, idonsa dake jajir har yanzu ya d'ago yad'an kalleni, jijiyar kansa dukta tashi rud'u-rud'u. saida yad'an lumshe idanu kafin ya motsa la66ansa ahankali yace, “kici abinci inji inno”. Dukda maganar taban haushi haka na danne, wato inji inno ma ba injishi ba ko?. Sakkowa nayi k'asan lallausan carpet d'in, d'aya bayan d'aya na bubbud'e kulolin da kwanikan, a rai na ina tunanin ina zamu kai wanna abincin haka?. Tashi nayi zuwa ga show glass d'in dake falon, wadda aka jera mugs and glass cups, mug d'aya na d'akko, naje wajen wanke hannu dake a wajen dinning, Wanda babu tebirin cin abincin ba'a sakaba, bansan dalinsa nak'in sakawarba, wanko mug d'in nayi na had'o kayan tea a ciki dake a wajen show glass d'in suma, na zubo ruwan zafi daga dispenser na dawo, yana kwance yanda na barsa, yanzuma garda su lumshe idanu yanata shafa kan yaron zuwa bayansa. Na kallesa a d'arare Dan yaune karan farko dazan aikata hakan, komi yake buk'ata yakan yi da kansa, ko ruwa wannan inhar bana manta ba bai ta6a cewa na d'auka masaba, sometimes ma sai idan yasaka Samha ko Sauban su masa Abu saini na tashi nayi idan naga rashin dacewar hakan, amma dai dakansa yace Munaya yimin kaza, gaskiya bai ta6aba. muryata na rawa nace, “bismillah”. Shiru kamar bazai bud'e idonsa ba saikuma ya bud'e d'aya yad'an kalleni ya kauda kansa. cikin k'asaitar nan tasa yace, “miyasa?”. “miyasa kuma?”. ‘nakuma maimaita maganar ina k'ok'arin janye hannuna’. Carab ya rik'e hannun nawa, ni tsoroma ya bani, na kalli hannunsa da nawan ga mug cikeda ruwan zafi yanata turiri, kuma zafin yana ta6amin gwiwar yatsuna, idonsa a lumshe har yanzu, idona harya fara tara kwalla, nayi alk'awarin koda hannun zai toye gaba d'aya bazan tanka masaba, ai yasan abinda yake dai-dai da akasin haka. Saida mukayi 1minute a haka kafin ya maido face d'insa inda nake yana kallona, ya d'age gira d'aya yana fad'in “da zafi ne?”. Humm lallai Galadima akwai rainin wayo, na fad'a a zuciyata, janye idona nayi daga kansa na maida kan Abdurraheem dahar yanzu yake kwance a bisa cikinsa. Ya yamutse fuska yana sakin hannun, cikin basarwa yace, “inason jarumta”. Had'iye kukan dake k'ok'arin tahomin nayi, na ajiye Mug d'in na cigaba da zuba masa farfesu a k'aramin bowl batareda nayi koda tariba. Tashi yay zaune yana jije lips, yayinda hannunsa ke rik'e da yaron, d'ayan kuma ya dafe saitin zuciyarsa, a wahalce yake fisgo numfashi kafin ya fesoshi, tun kuma d'azu na lura da hakan, kalmar zafi daya fad'amin na shiga fassarawa, har na fahimci da manufa ya fad'a, hakanne ya Sani murmusawa batareda na d'agoba ina zuba masa farfesun nace, “tabbas duk zafi sunansa zafi, amma akan samu banbance-banbance wajen banbancesu, wani zafin a gangar jiki muke jinsa, wani ko tawani sashen jikin ake samunsa, wani zuciya, wani rayuwarma gaba d'aya Ce ke tsintar kan a zafi, saidai babu zafi mafi rad'ad'i daya kai na Mutuwa, idan da zamuyi nazari zamu fahimci rayuwa tana a tsare ne mataki-mataki, sannan iri d'ayace ga kowanne launin halitta na mutum ko aljan ko dabba, Dan mukan tainci kanmune akusan mizani d'aya, dukda ubangiji ya banbantamu ta halitta da ayyuka da tunani ko nace kaifin basira, ko'a jinsi launi biyune, akwai namiji akwai mace, dukkan rayuwa takan farane da mafari yalla6ai” na d'ago ina sake mik'a masa mug d'in tea d'in again, a mamakina a yanzu saiya kar6a, na lashi lips d'ina na k'asa ina gyara zama sosai da maida hankalina wajen juya kunun dana zuba a cup da tsokali, cikin nisawa nacigaba da fad'in, “mafarin rayuwa shine dasuwar bawa a cikin mahaifiya, mukanyi wannan rayuwarne a cikin halin su wanene mu? daga nan sai matakin haihuwa, shigowa duniya a bisa bigiren wane ahali muka kasance, dukkan ahalin daka Sani sunada matsalarsu, saidai tawasu tafi tawasu zafi, daga ranka ka iso filin gwagwarmaya wato duniya, shikenan littafinka dayazama rubutacce tun a cikin mahaifiya saiya fara aiki, mala'iku masu kula da fitar numfashi su dasa alk'alaminsu, masu kula da abinci suma haka, masu kula da ruwa ma haka, masu kula da magana ma haka, masu kula da kallo ma haka, masu kula da ji ma haka, masu kula da duk wani motsinka ma haka, tafiya, zama, kwanciya dadai sauransu, kowa ana haihuwarsa tsaftatatccene, iyaye suke fara juya akalar rayuwa, walau mai k'yau ko sa6aninta, (kaga kenan akwai hisabi tsakanin iyaye da y'ay'a ma kenan?) daga nan rayuwa zata cigaba da yad'o kamar d'an duma, tun ana maka, harka koma koya, harka fara iyawa da kanka, harma ka kware ka koyama wani, (wanne ka iya? ko ka koya? yarage ruwanka) duk Wanda kaga an masa a farko to tabbas za'a k'ara masa a k'arshe, kodai silar tsufa, ko ciwo, kokuma iftila'in rayuwa, kokuma na k'arshe shine hidimar gawarka, a dukkanin dunk'ulalliyar rayuwar da kowanne bawa yakanyi zakaga cike take da k'alubale masu zuwa da zafi kala-kala, yalla6ai kasan mike taushe wannan rad'ad'in zafin kuwa?”. nayi maganar ina d'ago ido na kallesa. A mamakina sainaga ya girgiza min kansa. na murmusa ina janye idona daga kansa na maida ga kofin tea d'in ina masa alamar yasha mana. Yamutse fuska yay irin kalar tausayinnan. Nima sainayi kwal-kwal da ido kamar zanyi kuka, na had'e hannayena waje d'aya alamar rok'o🙏🏼.. Lips d'insa yad'an ciza kafin yafara shan tea d'in. Nayi salute nashi ina masa jinjina👍🏻. Basarwa yayi, nima saina kad'a ido ina tunzura baki gaba, sannan nacigaba da fad'in, “Abinda ke taushe wannan rad'ad'in zafin shine *_HAK'URI_*. hak'uri muhimmun sinadarine dake jagorantar garkuwar jiki ta kowacce launin halittar jiki na d'an Adam, walau a fili take ko a 6oye take, saidai babban makarinsa da taskar adanashi shine *_ZUCIYA!_* a duk lokacinda k'arfin zuciya ya raunana to zaka samu madarar hak'uri ta salwanta, idan zafi yanata yawa babu wannan hak'urin bugu d'aya take duk wani ma'adani na cikinta saiya tarwatse, saikaga an rasa ayyukan jiki dana ruhi, shikenan wane yazama labari. daga lokacin da rad'ad'in fitar rai ya kusanci bawa dukkan mala'ikunan da suka kasance tare dakai a randa kazo duniya saisu fara janyewa daga gareka, wani bawan kafin ranar mutuwarsa zakaga ya daina cin abinci, hakan na nufin mala'ikan dake kula da abinci ka yagama aikinsa, domin ya zagaye duniya kaf duk yawan abincin dake cikin ta babu rabonka koda kwayan gero ne, ka gama cinyewa, wani kafin ranar Mutuwa ya daina shan ruwa, aikin mala'ikan dake kula da ruwa shanka yagama k'arewa kenan, duk yawan koramu da tafkuna na duniya bakada sauran rabo na ruwa, ka shanye naka, wani kafin Mutuwa ya daina magana, mala'ikan dake kula da furucinka yagama aikinsa, babu sauran wata kalma data rage harshenka ya furta, wani kafin Mutuwa ya daina ji, mala'ikan dake kula da jinsa ya gama aikinsa, babu wata kalma data rage kunnensa zaiji, wani kafin Mutuwa ya daina gani, mala'ikan dake kula da ganinsa ya gama aikinsa, kwayar idonsa bazata sake kallon wani abuba, wani kafin Mutuwa ya daina tafiya, mala'ikan dake kula da tafiyarsa ya gama aikinsa, haka-haka wad'annan mala'ikun zasuyita ja baya suma barinka, har yarage sai mai kula da fitar numfashi kawai, daga ranar da UBANGIJI yace yana buk'atar ganinka shikenan takuma k'are, sai rundinar mala'iku su had'u su takewa kwamandan mala'ikan d'aukar rai baya, idan kai mutumin kirkine fararen mala'ikune, idan na banzane mala'iku masu azaba zasu take masa baya, sauran al'amari kuma sai Wanda ya haliccemu yasan ya zata kasance😭. zakasha mamaki idanfa nace maka duk wannan zafin k'aramin zafine acikin kashi-kashin na abinda ya shafi haluttu, shi wannan zafin ana kiransa zafin na za6in kai, kokuma zafi na a haka tsarin yazo, ma'ana kaine ka had'ama kanka wannan zafin, kokuma wanine ya had'a makashi. Abu na biyu shine zafi na rad'ad'in Mutuwa, dolene kowa saiya d'an d'anashi, walau kafiri ko Musulmi, saidai akwai banbance-banbance na awanne tsari ka koma ga ALLAH, ba wannan zafinne kawai ke jiran d'an Adam ba, akwai zafin na *_BARZAHU_* shi ake kira kwanciyar kabari, mika tanada, mi zaka tarar shine abin tambayar, wannan kam ALLAH ne mafi sanin wad'anda zasu d'and'ana wannan zafin (ALLAH ka datar damu😭)”. Akan la66a Galadima ya amsa da amin, Munaya ta share hawayenta, ta cigaba da fad'in sai zafi mai gaba d'aya, shine na makoma, *_WUTA KO ALJANNA_*, yalla6ai wad'annan jimullar zafin ga d'an Adam tilas ne, na cikin rayuwa shine zafin da zaka iya controlling nashi ta hanyar hak'uri, to Ashe bai kamata ka tasirantar da wannan zafin ya cigaba da k'onaka ba, musamman idan zakayi dubi dawasu ni'imomin da ALLAH yamaka a cikin wannan zafin, ka kasance mai yawan hak'uri saikaga kanka cikin masu yawan riba, wlhy ta wannan hanyarne kawai zaka zama mai *_NASARA_* akan mak'iya ni..........”. Maganata ta katse saboda knocking d'in k'ofar da akayi, kallon juna mukayi ni da shi, yay wani luuu da idanunsa ya lumshesu, hakanne ya sakani bada izinin shigowa kawai batare da na jira amsa daga garesa ba. Sarkin k'ofane ya shigo, ya zube yana gaishe mu, nice kawai na amsa, boss kam hannu kawai ya iya d'aga masa, yay mana ya jiki again, nanma nice nakuma amsa shi, cikeda girmamawa yace, “ranki ya dad'e yalla6ai harun ne ke buk'atar iso”. Saida gabana ya fad'i, na had'iye wani yawu mai kauri ina kallon galadima dayay biris damu yanata shafa kan d'ansa, bud'e idonsa jajaye yayi akan Sarkin k'ofa, ya jinjina masa kai alamar ya shigo dashi. Kallonsa nayi tamkar zanyi magana saikuma nai shiru, a raina ina mamakin wannan munafukin dami yazo kuma?..... ban kai k'arshen zancen zucin ba Harun yay sallama, nid'ince dai na amsa cikin danne zuciya da fushina. Ya zauna fuskarsa d'auke da murmushi. Nima saina saki tawa ina fad'in, “barka da hantsi ranka ya dad'e”. “Barka dai gimbiyarmu, ya jikin ki dana yalla6ai?”. Na kalli Galadima dayay shiru kansan jingine da kujera ido a rufe, “da sauk'i”, na fad'a ina mik'ewa na koma saman kujera, dan bazan ta6a barin falonba sainaji uwarmi ya kawosa. Ya amsa da “masha ALLAH, ALLAH ya kiyaye gaba ya k'ara lafiya”. “humm” na fad'a ina amsawa da “Amin dai”. Hankalinsa ya maida ga Galadima, “Sameer ya jikin?”. Bud'e idonsa yayi shima, ya ajiye mug d'in hannunsa a teble d'in dake gefen damarsa, batare da yace uffanba ya sauke ajiyar zuciya yana taunar lips. Banga alamar damuwar rashin amsawar tasaba a fuskar Harun, dan yariga ya saba da halinsa. Saidai idonsa k'uri akan Abdurraheem dake cinyar Galadima d'in yana barci, mik'ewa yay yana fad'in, “my son zo mu gaisa ko?”. Ganin haka nima nayi azamar mik'ewa nakai ga Galadima kafin shi ya isa, na d'auke Abdurraheem d'in ina fad'in “ai barcima yake ranka ya dad'e”. Ba Harun ba hatta da Galadima saida yaymin kallon mamaki, nakoyi cid'in-cid'in da fuska yandama bazaice nabama Harun d'inba. Baki ya bud'e kamar zaice wani Abu saikuma yay shiru yana kauda kansa daga kallona, nima saina ta6e baki ina barin falon da harar Harun ta gefen ido. Gaban Harun ya fad'i, mi yarinyarnan take nufi?...... Kafin ya lalubo amsar ya tsinkayi maganar galadima yana cewa, “sorry Harun, kasan har yanzu a tsorace take, duk wani motsinsu akan idontane”. Murmushin basarwa harun yayi, yace, “ai dolene hakan ranka ya dad'e, abinne akwai tsoratarwa, wlhy jiya tashin hankalinnan ne yasaka azababben ciwon kai rufeni, shiyyasa ko ganina ba'ayiba, yanzu police d'in ina suka samosu?”. “humm” Galadima ya fad'a cikin tsananin taune lips da k'unar zuciya, ya bud'e baki a hankali zaiyi magana nida ke bayansu basu saniba nai saurin tareshi da fad'in “a hannun wasu munafukaine ranka ya dad'e, ai koni daza'a bani baiwar nan da aka kama da yaran wlhy saina tsoma kanta cikin drum d'in ruwa harsaita daina Numfashi zan barta, kafin sannan kuma nagamajin labarin Wanda ya sakata, amma shi my boss ai a station suka zauna har aka kawo yaran, badasu akaje farautarba”. Tsuramin ido Galadima yayi cikin tsagwaron mamaki, miyasa to zanzo na kasa na tsare dukkan wani motsin Harun d'in? ya kula satar yaran tana Neman ta6a tunaninta takasa banbance Wanda zata zarga, ai Harun yawuce ya 6oye masa wani sirri na sashen rayuwarsa, tun da babu abinda bai saniba na baya, saidai abinda ba'a rasaba kam, danne ransa yayi ya nuna hakane, yabari har Harun d'in ya tafi sannan yaji dalilinta. Ina kallon Sassanyar ajiyar zuciya da Harun ya sauke a 6oye, sannan yace, “ai police d'in sun cancanci Babar k'yauta, shiyyasama na shirya musu ita, sunyi aiki irinnan jaruman masu tsaro”. “hakane wlhy ranka ya dad'e ”. Na fad'a cikin murmushi. Dukfa yanda Harun yaso bugar cikin Galadima yaji yanda abun yake, na kafa na tsare, dayayi tambaya nike bashi amsa, saiya d'auka kodan Galadima bashida lafiyarne shiyyasa bai iya amsawa, tun da tunda ya shigo baice k'ala ba, kuma yasan yanayin ciwonsa, a baya ma shikan bashi taimako, baidai tsinci komai ba yay mana sallama ya fita, da k'udirin anjima ma zai dawo ne. A sace na raka bayansa da harara, sannan na kalli Galadima na basar, dukda kallon tuhuma dayake jifana dashi kuwa. Wani farfesun na sake zuba masa na mik'a masa. Batare da ya kar6aba cikin k'ank'ance idon bala'i yace, “mikikayi haka? kinsan waye Harun a wajena?”. Kaina na girgiza masa. Yaja tagwayen tsaki yana hararata, “halan satar yaranki yafara shafar tunaninki ne? kina tunanin akwai abinda Harun zai iya gazaji daga sirrina?”. Na d'an ta6e baki ina jawo teble d'in gabansa, na d'ora bowl d'in dana zuba farfesun, baki ya bud'e kamar zaiyi magana saikuma yay shiru. nima bance uffanba na ajiye masa sannan na koma k'asa Na zauna na zuba sabon kunu nahau sha. Kwafa yayi, yace, kinma maidani d'an iska ko?”. “Hummm” na fad'a kawai, naimasa kallo d'aya “yalla6ai wani karatun akan barsane a yanda yazo, sai idan lokacin fasaarashi yayi amasa fashin bak'i, nasan darajar alak'ata dakai batakai koda rabin tsakaninka da Harun ba, domin ni alak'ar wucin gadice ta had'amu, k'iris ma ya rage ta k'are, saidai inason nabama y'ay'ana kamar yanda ka fad'a kariya koda sau d'ayane a rayuwarsu kafin na barsu, dan haka maida wuk'arka a kube, lokacin zareta baiyiba, sometimes kalmar Mahangi da mai hange takanyi kamanceceniya, dan bakowa ke iya rarrabata wajen fasaara ba, amma kalmomine duka masu harshen damo, wani k'alubalen saida tunanin mai zurfi, wata k'oramar ruwan mutanen dake zagaye da ita sukanyi imani bazata balle harta cisu ba, saboda sun yarda sud'in masuntane da kullum suke rayuwa cikin wannan k'oramar, abin mamaki saikaga wataran an wayi gari da mutanen da muhalansu duk wannan ruwan ya had'iyesu, abinda basu ganeba bakowacce irin alak'a bace ake kulla amana da ita, wani farin idan yashiga cikin fari banbance k'arkonsa saidai ALLAH”. Tashi nayi nai shigewata bedroom d'insa. A fusace shima ya mik'e zai bini, kad'an yarage ya zubda farfesun dana ajiye masa, ALLAH dai ya kiyaye ya shallakesa ya wuce. Hucin mutum kawai naji a bayana, hakan yasani waigowa da sauri, hannu ya dunk'ule zai kaimin naushi, nai azamar fad'awa saman gadon ina zaro ido waje, a lallai Abu ya girmama, nikuma miye nawa da zai sauke fushinsa a kaina? nai maganar a zuciyata. Janye hannunsa yayi yana ciza lips d'in sa da k'arfi, idonsa dukya kuma rinewa, ya dunk'ule hannun ya daki d'ayan dashi, muryarsa har rawa take yace, “Miyasa zaki kuma hargitsan tunani ne? Minene laifin Harun shikuma? kuna nufin duk Wanda na yarda dashi shine mak'iyina? Kai impossible wlhy, Munaya wakikema aiki a kaina? ya rankwafo kaina, kaikace cinyeni d'anya zaiyi, saikace zaki yaga bandar nama, da k'arfi yace, “bazaki sanarmin ba saina k'arar da numfashinki ne waishin Ubanwa ke fad'a miki wad'annan maganganun da kike d'aureni dasu a ko yaushe?!!!”. Ya k'are maganar cikin tsananin tsawa da k'araji. Ba k'aramin firgita nayiba, badan karnayi k'arya ba danace har wutar bala'i Nagano a idonsa tana ci, wannan bawa akwai zuciyar tsiya, idan zai zama jami'in tsaro da k'asarmu ta amfanu da yawa......... Da k'arfi ya girgizani, saboda ganin saboda rainin wayo tunanima na tafi.......... A firgice nace “yi hak'uri zauna zan fad'a maka”. na fad'i hakanne dan kawai ina ganin itace mafitar dazan nema ya fasa had'iyeni. a mamakina kuwa saiya tashin ya zauna yana dafe k'irji hawaye nabin kumatunsa. Tsantsar tausayinsa ce ta kamani, na tashi na d'akko ruwa na dawo kusa dashi na zauna, addu'oi na shiga tofawa a ruwan, yana zaune dafe da kansa, da alama kuka ma yakeyi, dan ajiyar zuciyar da yakeyi ta yawaita. Saida na gama na dafa ka fad'arsa, tamkar bazai d'agoba saikuma ya kalleni, ruwan addu'ar na basa, babu musu ya kar6a ya shanye, duk da baima san mita bashiba, idanma poison ne dai gara ma yasha ya mutu ya huta. Mintunansa biyu zuwa uku dasha yafara sauke ajiyar zuciya mai k'arfin gaske, saiya zame kuma ya kwanta, kafin kacemi barci ya saceshi a haka. nima ajiyar zuciyar nayi ina girgiza kai da share hawayen dake silalomin, ina rok'on ALLAH ya kawoma wannan bawan nasa sauk'i da rangwame cikin gaggawa da warwarewar al'amura. Dagashi har yaran tausayi suke bani, nayi zurfi a tunani wayarsa tayi ring, kamar zan share saikuma Na tuna maybe Momma ce, tashi nayi zuwa inda wayar take, aikam dai itace, nayi picking jiki a sanyaye, dan tunanina kota gamajin komai, amma sainaji sa6anin haka, da y'ar raharta ma tace, “Muh'd duk hidimar sunance haka?”. “Uhm Momma bashi bane nice”. “a'a d'iyata kece?”. “eh Momma, kuna lafiya? ya jikin Abie?”. “Alhmdllh d'iyata, ya k'arfin jikinki kema? ina yaran?”. Gabana ya fad'i, Na had'iye wani yawu da k'yar, cikin in ina nace, “lafiyar kowa k'alau Momma, shima y... yana barcine”. Dagacan Momma ta murmusa tana gyara zama a harabar asibitin, dan batason Abie yaji wayar da zatayi, tace, “humm d'iyata kema 6oyemin zakiyi kenan? yanzu koda mutuwa yaran sukayi dashi kansa kowama saiya shiga fargabar gayamin?”. Na had'iye yawu dak'yar, “kiyi hak'uri Momma, ki gafarcemu”. “Bakumin laifin komaiba ni, hakan da Muh'd yay shine dai-dai, dan lokaci yayi dazai daina zama jiran sak'on mak'iya ko zuwansu, shine yakamata ya fita farautarsu domin kawo k'arshen komai, na yarda dake 100% Munaya, nakumayi imani insha ALLAH kece zaki sauyamin yaro daga k'uncin dayake ciki zuwa farin ciki, tamkar yanda Na fad'a miki tun farko karki ta6ama Muh'd sanya ko nuna tsoronsa, lokacin dazaki kwantar masa dakai kizama kowacce irin mace a agidan mijinta har yanzu baiyiba, kada ciwonsa yasakaki fargabar fad'a masa gaskiya, rayuwa da mutuwa duk Na ALLAH ne, ko ayanzu Muh'd yabar duniya bazanyi bak'in cikiba, domin ya nuna musu shi jarumine, kuma ya haifi wad'anda zasu iya zama magadansa su sauya komai koda ba'aso, nanda kwanaki biyu komai ya gama lafawa ki tabbatar kin masa maganar tafiya wanka gida, wannan shine target d'inmu Na k'arshe akan rayuwar zaman aure na dindin, kowacce irin birkicewa zai miki akan bazaki jeba, kema ki birkice masa, dan nasan abinda yafaru zaisashi dagewa akan yaran bazasuyi nesa dashiba, idan kuma har aka cigaba da tafiya a haka, kowane irin dana Sani zai iya biyo baya”. Momma ta share hawaye dake kwarara a idanunta, taci gaba da fad'in “ALLAH yayi miki albarka Munaya, dake da abinda kika haifa, yanda kikamin biyya wajen k'autata kar6ar Abu mai wahala (duk da bani na haifekiba) kema ALLAH yasa y'ay'anki sumiki biyyaya fiye da wannan, ALLAH yasaka hannu adukkan lamarinki keda mijinki da sauran y'an uwansa, nusar dashi abinda duk baki gamsu dashiba shine zai rage ma zuciyarsa baraza, dan tarawar yagani a lokaci d'aya shine mafi had'ari Munaya, zuciyarsa zata iya bugawa a lokacin, kiyi hak'uri nasan bak'yajin dad'in zama da Muh'd ko kad'an, domin ni kaina mahaifiyarsa wataran gaza gane kansa nakeyi, amma inaji a jikina akwai sauyi maiban mamaki dazai zo ya rusa komai, ki sameshi fiyema da yanda kikeso, ALLAH yayi muku albarka, idan ya tashi ki kirani naji ya jikin nasa”. Bata jira nayi magana ba ta yanke wayar, da alama kukane yaci k'arfinta. nima saina fashe da kukan ina kallon Galadima, insha ALLAH zan cikama baiwar ALLAHr nan burinta, koda ace mun rabu dashine, dan maganar gaskiya bazan iya rayuwa da mutum murd'ad'd'e mara yarda irin Galadima ba, labarinsa kawai kukeji, amma halinsa saika zuna dashi, Mara hak'uri zai iya gundurarsa ne cikin awanni biyu kawai, dan zaka dinga kallonsa a matsayin mai wulak'anci ko dizgi, girmankai da sauransu. Na sauke ajiyar zuciyarsa ina maida kallona ga Abdurrahman dake motsin tashi, nasan dukansu saisun tashi inhar d'aya ya tashi, saina lalla6a na kwanta kusa dashi na saka masa nono a baki. ******************** Har akayi la'asar Galadima bai farkaba, Nuren yazo shida Sauban, da Saleem har sau biyu suka iske yana barci, hakama Mom da inno da mama Fulani. Gashi su inno 4:30pm zasu wuce ma, laraba tazo tama yaran wanka, dan tuni sun farka, Nima nakumayi sannan naci abinci, kaina ciwo yakemin sosai, dan haka Sauban yafita ya samomin Magani nasha na kwanta, munyi sallama dasu Mom, zasu dawone kawai idan Galadima ya farka kafin su tafi. yaran kam duk d'insu suna can an kaima papi su tun d'azun. Nidai barci yay awon gaba dani, daga nankuma bansan wainar da aka cigaba da toyawa ba a gidan. ******************* Bayan la'asar kad'an Galadima ya farka, ganin shi kad'aine a d'akin ya tashi zaune bakinsa d'auke da addu'ar tashi barci, jin k'irjinsa yayi sakayau yasaki babu nauyin kamar d'azun, saidai abinda ba'a rasaba, yatashi zuwa bathroom yay wanka da alwala. Sallan zuhur da la'asar ya rama, tareda addu'ar neman sauk'i akan wannan lamari da samun k'arfin zuciya, dolene saiyayi yak'i da dukkan abinda zai zama makamin barazana a agaresa inhar da gaske aikin zaiyi, falo ya fito bayan ya kimtsa, zamansa da mintuna baifi 2 ba saigasu inno. Basu jira isoba suka shigo, a zatonsu yana bedroom yana barci, sunsan Munaya kuma tana d'akinta tana barci tunda daga can suke. ganinsa a zaune ya saka fuskar kowannensu fad'ad'a da murmushi. Shidai kallonsu kawai yake d'ai-d'ai. Inno ta mangari kansa tana fad'in “ja'iri baka sanmu bane halan?”. Hannunta ya rik'e yana kallonta, cikin maganarnan tasa ta k'asaita yace, “Inno wai ina zakuje ne?”. “inda muka fito mana”. Inno tafad'a tana zama kujerar kusa dashi. “saikace wad'anda ake kora?”. “A'a wazai koremu nida gidanmu, komawar dai ne yafi cancanta, dan takawa ma yace a gaisheka basai ya shigoba, zakuyi waya, idan ka murmure kaje yana nemanka”. “To shikenan ALLAH ya tsare hanya, mun gode sosai da sosai”. “Amin” inno tafad'a tana shafa kansa ta ciga da kwararo masa addu'oi shida matarsa da yaransu, falon kowa tana amsawa da amin, itama mom tayi nata. Yace, “mom hada ke wai?”. “eh mana Sameer, zaman mi zanyi to? tunda ALLAH ya iyakance komai cikin sauk'i, nanda y'an kwanaki kuma basai na zagayo naga masu jego ba da jikin naka, a dai dunga kulawa sosai, gasu laraba nan da bayi 2 anbar muku, dukdai wata kulawa insha ALLAH zasu taimaka wajen badata akan yaran, dan yakamata dukkan bayi da kuyangin sashen nan naka ka sallamesu kawai”. Kansa ya jinjina mata alamar amsawa. A gurguje sukad'an kuma tattaunawa da kwantar masa da hankali suka fito, dukda yaso musu rakkiya suka dakatar dashi. Abincin da mom ta zuba masa takumace yamata alk'awarin zaici ya dage yaci sosai, sannan Sauban daya dawo rakkiyarsu d'auke da y'an uku shida bayinnan biyu yabashi magani yasha, kar6ar Amaturrahman yayi, Sauban kuma na zaune dasu Abdurraheem yana musu wasa wai dole sai sunyi dariya, (nace, “aiki jaa kenan, inba dariyar k'udaba ta jarirai idan suna barci keyi aiko ka dad'e baka ganiba Uncle triplets😂). Galadima ma madai yatsansa d'aya ya saka cikin hannun Amaturrahman yana wasa dashi, dukda idonsa a lumshe yake ya jingina kansa da kujera, maganganun Munaya na d'azun kawai yake nazari dalla-dalla. Ana cikin haka Samha tayi Knocking, Sauban yace ta shigo, saida ta gaida Galadima damasa ya jiki. Ya amsa mata batareda ya kalleta ba, tareda tambayarta Khaleel fa?. Tace, “yana 6angaren Ummu hasheem”. Baice komaiba, itama ta k'araso ta d'auki Ammaurrahman data rik'e yatsansa gam tak'i saki.. d'agowa Galadima yay yana kallon yarinyar, Samha dai dariya takeyi, har Sauban shima ya farga da abinda ke faruwa ya shiga tayata. Galadima ya zare yatsansa yana murmuahin gefen baki da lakatar hancin Amaturrahman. Har Magriba suna nan sun shashance akan yaran, yayinda Galadima ke zaune yanata cud'awa da tantancewa, lokaci-lokaci yakan kallesu dagasu har yaran. Tunda ya tambayesu Munaya sukace tasha Magani tana barci bai sake tambaya ba. ******** Ban tashiba saida suka fara kuka, a time d'in har magrib tama wuce, nagama shayar dasu na lek'a Galadima, na iske doctor jalal tareda Dr Yaseen da Akash Wanda yake shirin komawa gobe, sai Muftahu da Nuren. Muka gaisa dasu suka kuma tambayata jikinsa? na Amsa musu da Alhmdllh. fitowa nayi na barsu, da aka kawo mana abinci ma can nace akai musu, Sauban yazo ya kwashi yaran bisa Umarnin Galadima, doctors zasu kuma duba lafiyarsu. ★★★★★★ Tunda Harun ya fita saiya kira wata Number lokacin daya k'arasa d'akinsa, dukkan abinda ya faru ya labarta mata, daga can tace k'aryane bahaka akaiba, ita an sanar mata lallai da Galadima aka kar6o yaran, babu wasu police, amma itafa kamar tafara saka alamar tambaya akan wannan ficikar matar tasa. Harun yace, “haba dai, wannan y'ar yarinyar mizata iya, akwai dai abinda bamu saniba, yanzu dai kibari zamuyi maganar daga baya, zand'an bincika yarannan danni na lurama kamar ba wad'anda muka saka bane sukayi aikinnan?”. “sunefa gaskiya, abinda dai na lura dashi sun had'a aikin da wasune, shiyyasa suke 6oye mana Kansu, tunda kaga mudai baiwarnan bamu muka sakata ba, amma shi namijin yana cikinsu, nasan sunyi luff ne sai k'ura ta natsa su fito”. “ok shikenan to, zandai sake bincikawa, dan Sameer yanada wayo, shiyyasa naso bugar cikinsa akan batun, amma wannan shegen k'asaitar tasa ta rainin hankali ya hanashi tankamin, sai matarce ke bani amsa”.. “karka damu zamu sauke masa shine ai”...............✍🏻 🤣abin dariya, ku a naku zaton yaranku sun 6oye Kansu be?, to suna hannun Galadima, lafiya kawai muke jira ya samu ya yagalgalasu kuma ya cafkoku munafukai🙄😏. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu._*😭🙏🏼 [8/21, 8:44 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣8⃣ .................Har yamma Galadima bai dawo gidanba, abincin ranama da aka ajiye masa sai d'aukeshi akayi, sainaji inajin tausayinsa, dan nasan yanacan ba zaune waje d'ayaba, yawan harkoki dayakeyi kansa kullum yake yawo tamkar wata motar haya, shidai kullum burinsa ya iya d'aukar nauyin ahalinsa, bai yarda zama rago ko jira daga waniba koda ace papi ne, ya yarda yasha wahalar nema amma ta gumin halak, sa6anin matasanmu da kullum burinsu nakan gwamnati ko alhajin anguwarsu ko d'an siyasa, ko alhajin da yafi kowa arzik'i a danginsu. Akwai wata kalma da Galadima yata6a fad'ama sauban Wanda akulum Na tunata tana k'ayatar dani. Lokacin inada tsohon cikinsu Amaturrahman, da yawan cin abincinnan Na masifa, aranar jikin Abie yad'an motsa, sai yakasance nikad'ai aka bari a gida sai hadiman gidan, cikin barci yunwa ta addabeni, hakan yasani farkawar dole Na sakko k'asa da k'yar, kitchen Na shiga nasami madara Na d'umama kafin kuku yad'an girkamin wani Abu, fitowata daga kitchen d'in keda wuya sai Galadima da Sauban suka shigo, da alama ya tuk'osane, dan idan yana cikin damuwar tashin ciwon Abie Momma hanashi driving takeyi. Da mamaki Sauban ya kalleni da cup a hannu yana fad'in “Yanzu nan Aunty duk hadiman gidannan saikin shiga kitchen da kanki a wannan halin? Aiko yau saisun gane kuransu”. Ya tafi fuuuu cikin fushi saina dakatar dashi ina murmushi. Nace, “A'a Yaa Sauban, kabarsu please, nice ban sasunba nayi da kaina, amma aiga shican nasaka kuku wani aikin”. Galadima dake zaune saman kujera ya d'aura k'afa d'aya kan d'aya idonsa a lumshe tamkar baisan mi mukeyibama ya bud'e baki cikeda k'asaitar nan tasa yana fad'in, “Ai duk Wanda ya dogara da k'arfin wani to lallai nasa na cikin jerin k'arewa a sahun marasa amfani, dan zai dawwama cikin bibiyar samu daga waninsa shikuma bai amfanu datasa fik'irarba, kazama mai k'arfin zuciyar gina kai ba zaman jingina da bangon waniba”. Yana gama fad'ar haka ya tashi ya haye sama, dagani har Sauban da kallo kawai muka bishi, kowa na fassara zancensa dalla-dalla, ni abinda na fahimta kai tsaye bada Sauban d'in yakeba, akwai abinda yafaru daga can inda suka fito, amma saiya za6i mu yamana sharhi bisa dalilin dashi yabarma kansa Sani. (ALLAH dai ya ganar da matasanmu domin tashi su nemi na Kansu ta hanya mai k'yau basu cigaba da dogaro a bangon wasuba.👏🏻😢). Tun d'azun yake tsaye akanta amma bata saniba, ta Lula duniyar tunani mai zurfi, ga Abdurrahman dake gefenta yanata mutsu-mutsu da k'ananun kuka amma batama jishiba. Agabanta yay wani durk'uso mai birgewa, yakai fuskarsa daf da tata yana hura mata iska a saman ido zuwa hanci. Wata sassanyar ajiyar zuciya na sauke tareda dawowa hayyacina cikin zabura, yay azamar damk'e hannuna da fad'in “My Mata!?”. Ajiyar zuciya na sauke tareda dai-daita dan fahimtar shine, na zuba masa idanu cikin mamaki nace, “Yaushe ka shigo?”. Murmusawa yayi sannan yamik'e daga durk'uson dayay agabana, batareda ya bani amsaba ya fara k'ok'arin cire farar rigar suit d'insa. Mik'ewa nayi na taimaka masa, sannan nadawo gabansa na warware tia.. 'Din da bottoms d'in pink d'in rigarsa ta ciki. Sai wani faman lumshe idanu yake da bud'esu akaina, bansan miyake tunaniba. Ina cire bottom d'in k'arshe na rigar ya rik'e hannuna, idanu na d'ago na kallesa, ya sakarmin wani k'asaitaccen murmushi yana matsoni jikinsa sosai, a saman la66a ya furta “Kinyi k'yau sosai, amma mikike tunani haka?”. Da mamaki na kalli kaina, sanye nake doguwar rigar shadda milk color, anmata simple aiki da brown d'in zare, an k'awatashi da stones, Wanda sune suka fidda ainahin k'yawun d'inkin, sai siririyar sark'a data kwanta a wuyana d'as, nayi d'aurin Maryam babangida daya kuma fidda ainahin suffata ta bahaushiyar asali mai rik'o da al'ada. Yanda nake bin jikina da kallo haka Galadima kebi shima da idanunsa, na maida kallona ga face d'inshi dake kadaran kadahan, bai d'aureba kuma babu walwala sosai tare dashi. Gira d'aya ya d'agemin sai kuma yad'an ta6e baki yanajan hancina da had'e yatsunsa biyu na k'arshe👌🏻alamar komai yaji. Nad'an murmusa ina k'ok'arin barin wajen dan naga alamar miskilawan suna kusa. Ruwa naje na had'a masa, na fito ina goge hannuna da towel. Durk'ushe na iskeshi gaban Abdurraheem da cup d'in ruwan dana ajiye danshi a hannunsa. Ya d'ago yana kallona dad'an murmushi a face d'insa, “kinsan minake gani a jikin Abdurraheem kuwa?”. Kaina na girgiza masa alamar a'a. Kallonsa ya maida ga yaran yana cigaba da murmushinsa. Yace, “Kamannin Abie”. Takowa nayi Inda suke Nima Ina murmushi mai sauti da fad'in, “Nadad'e da wannan tunanin a raina, saidai nabarma zuciyatane har sai randa zan gansu a waje d'aya, Ashe kaima kana lura?”. Wata y'ar dariya yayi, wadda tafi kud'i tsada awajensa. Yace, “My Heartbeat ALLAH kin iya haihuwa”. Ba k'aramar dariya maganarsa tabaniba, aiko nashiga k'yalk'yalawa. Shiko ya shagala da kallonta saboda birgeshi da dariyar tata tayi, burinsa dama yaganta cikin farinciki. Bayan na tsagaita da dariyar na kallesa Ina d'aga kai da kashe masa ido alamar kallonfa?. Mik'ewa yay tsaye ya dawo inda nake tareda rank'wafowa kaina yana dafa hannayensa biyu asaman gadon gefe da gefena. Kusancin namu yasakani d'anyin baya kad'an ina kallon cikin idonsa, yakuma matsowa, na matsa, yakuma again, Nina still na matsa, saida na haye gadon sosai shima yay balance yanda yake buk'ata sannan ya kwanto gefena kusan Rabin jikinsa a nawa, har lokacin idonsa na sark'e da nawa. Galadima yay bala'in Sanin sirrin kallo, inhar ya sark'e idanunsa da nawa duk wani hope d'ina nemansa nakeyi na rasa, yatsansa kawai naji saman la66ana yana zagayawa ahankali, santsin hannunsa Dana lips gloss d'in Dana sanya sunayin kamar susa, kasa jurewa nayi na lumshe idanuna a hankali. Galadima ya murmusa da bud'e baki da k'yar yana fad'in, “Kin cancanta, kin cancanta zama matar Muhammad Sameer Munaya, ked'inki da dukkan halayyarki irinta Muhammad Sameer ke buk'ata ga matarsa, ko ayarda ko kar ayarda nasan nama sauran maza zarra, dan matata tafi ta kowa, kinzama fitila mai hake gabana da bayana, kinzamarmin bango abin jingina lokacin danawa yanemi rushewa, shigowarki rayuwata na dai-dai da farkawata daga nannauyan barci mai cikeda rud'ani, nabaki dukkan zuciyata ki jani a sannu danna cigaba da ribantuwa da ni'imomin da ALLAH ya azurtaki dasu, I love you so much Munaya, I love you har a aljanna matsayin uwargidan matana”. Bansan lokacinda hawayen farinciki suka fara zirarominba, na bud'e idanuna dakai hannu saman kwantaccen sajensa ina shafawa a hankali, cikin wani yanayi nace, “Ka cancanci fiye da haka mijina, dan kanada zinariyar zuciya, kaimai tarin tsoron ALLAH ne dabin dokokinsa, a wannan zamanin samin matashin saurayi mai kud'ad'e da mulki a hannunsa dabaya wata masha'a abune mai wahala, baka kasance mazinaci ba, baka kasance mai shaye-shaye ba, ko sigari wannan bakasha, kulum cikin Neman halalinka kake Dason k'yautatama iyayenka dana k'asa da kai, kaimai ibadane, salla bata wuceka, mai yawan tsayuwar dare, mai yawan bitar littafi mai girma dake d'auke da zancen ALLAH ne, mai yawan sadaka da taimakon mutanen da bakuma had'a addiniba, bakada wata majalissa ta abokai daza'ace gaka cikin jerin masu cin naman wani ko zind'en wani, abinda ke gabanka da Wanda ALLAH ya halatta maka kawai kakeyi, mijina tayaya bazaka samu nasaroriba a rayuwarka? Ubangiji mai ni'imane ga dukkan Wanda ya ra6u samun ni'imar, babu wani Bawa dazai tsinci kansa a ta6ewa inhar yabi dokokin Ubangiji da koyi da manzon tsira, babu cuta mafi rad'ad'i da ciwo kamar bijirema Umarnin ALLAH Wanda ayanzu shike wahal da matasan duniya irinka, burunsu kawai su hole su mori k'uruciyarsu, sun manta babu tagomashi mafi k'yak'yk'yawan farashi irin morar k'uruciya bisa ga Umarnin ALLAH, yadda da k'addara, samu ko rashi, tsayawa matsayin da ALLAH ya ajiyeka, kaucema dukkan wata bad'ala, matasa sune k'ashin bayan al'umma, lalacewarmu ta saka al'ummar tafiya a karkace a halin yanzu, da'ace zamu gyara da kowa ya mik'e, dolene Momma da Abie suyi alfaharin samun d'a irinka, dolene Aunty Mimi da Yaa Sauban suyi alfaharin samun d'an uwa irinka, dolene su Samha dasu Amaturrahman suyi alfaharin samun Uba irinka, dolene k'asarka da addininka yayi alfaharin samunka, saidai duk nice nafisu sa'a da alfaharin samunka a matsayin miji uban y'ay'ana, inaji inama y'ay'yana su gaji k'yawawan hallaya da d'abi'u irinna mahaifinsu, saidai kash ina cike da fargabar tsoron kalmarnan ta bahaushe dakance *Bakowanne tauntsu bane ke raira kukan gidansu* wani tun a koyan tashi yake canja salo. Mijina ka more, ka matuk'ar morewa da k'yawawan hallaya, irinku kunada tsadar samu a cikin al'umma, da mutane zasu gane dasun fuskanci ba k'yawun fuska dana jiki bane abin alfahari, zinariyar zuciya da hallaya shine abin alfahari da d'agawa, saidai kash, burin samarin yanzu da y'ammata k'yawun fuska dana halitta, nauyin aljihun wayewa, basa tunanin mika tara mizaka taras, sannan mika barma bayanka da ahalinka Wanda ko bayan shekaru aru-aru tarihi bai Isa mantawa da kai ba, da inada dama sainabi matasan mata da maza dukna musu allura sunzama kamarka mijina, inasonka, ina sonka, zan fad'a a hankali, nafad'a da k'arfi, na fad'a da kuwwa, na fad'a da ihu agaban kowa kuma, Kaine duniyar Munaya, Kaine farincikin Munaya, zanta k'aunarka har randa nufashina zaibar gangar jikina, nakumayi fatan ganina a cikin matanka dake aljanna Muhammad Sameer”. Kasa magana Galadima yayi, sai bakinsa ke motsi alamar buk'ar firta wani Abu amma yakasa, idonsa yacika taf da kwalla, lallai hikimar zancema baiwace ga mace tagari, dashi kawai zata iya mallakar mijita babu boka babu Malam, dan gashi Munaya tasamu dukkan nasarori, ya rungumeni tsam a jikinsa tareda d'ora bakinsa saman la66ana, hawayen dayake rik'ewa suka gangaro saman fuskata. Banyi yunk'urin ko motsawa ba nabashi wuk'a da nama yayi yanda yakeso ni halalinsace..........😘👍🏻 *_Hummmm, lallai matar kwarai rabin addini, ya ALLAH kabamu damar zama matan kwarai ga mazajenmu😢🙏🏼_*. ******* Bayan shud'ewar wani lokaci muka dawo daga duniyar da muka tafi, kunya duk sai ta kamani, nakasa had'a ido dashi. Galadima ya murmusa yana kama hannuna zuwa hanyar bayi, banida za6in daya wuce na bisa kawai. Yauma dai tare mukayi wankan, nad'an sake dashi fiyeda d'azun da safe. Muka fito na taimaka masa da shafa mai, yasaka kaya marasa nauyi. Nima da taimakonsa na kimtsa sannan na sauka nemo masa abinda zaici dukda magrib ta gabato. Babu kowa a falon sai Khaleel dake homework. Sannu namasa shikuma ya gaisheni, nace, “Ina Samha my boy?”. Yace, “Aunty yanzu aunty Dhibiya tazo suka fita”. Agogon falon na kalla da mamakin fita a yanzun? Halan batasan Uncle d'inta ya dawoba?. Bance komaiba na wuce kitchen. Da taimakon kuku na shirya masa Abu mara nauyi, na had'o saman tire ina fitowa. Samha data shigo tad'an kalleni a firgice, nima kallon mamaki nake mata da tuhuma. Nace, “Daga ina haka?”. Kame-kame tafara na lalubo amsar dazata bani, wadda alamunta ke nuna k'aryace kawai zata fad'a. Girgiza kai nayi kawai nai gaba abina ina fad'in “Zanso sanin mike tsakaninki da Dhibya Samha? wannan abotar taku k'arfinta yafara tsoratani”. Banjira amsarta ba na haye saman benen. Gudun karya fahimci wani Abu na daidaita kaina tunkan na shiga, nasan inhar yasan raina ya6aci akan Samha ne sai taci k'aniyarta, nikam ba buk'atata ba kenan, nafison sanin tsakaninsu da k'awartata kafin na rabasu. Tsaye na iskeshi rik'e da abin salla, na ajiye tiren saman table d'in gaban sofa sannan na kalli agogo. Yanda banyi magana ba shima baiyiba, na nufi bayi nayo alwala nima, tsaye na kuma iskeshi yana jirana. Bayan mun idar da sallah na kallesa ina fad'in “Abinci yalla6ai”. Harara ya zubamin da rankwashi, na dafe wajen ina kwa6e fuska zanyi kuka. Yace, “Yalla6ai d'inan bazai bar bakinkiba ko?”. Dariya namasa da gwalo inaja baya, “Yo ba sunanka baneba”. “Da kika rad'amin ko? Zan kamakine ai”. Sanin halinsa yasani fad'in, “Toyi hak'uri bazan sakeba”. “Harkin karaya kenan?”. “Ba doleba, kamun nakane ai bamai sauk'iba”. Dariya sosai tabashi, amma ya had'iye abunsa kawai yayi murmushi yana cizar lips. Munaya tace, “Wato a rayuwa duk d'an Adam zaka sameshi dawata d'abi'a data zame masa jiki”. Kallona yayi da alamar tambaya, amma baice komaiba. Mik'ewa nayi tsaye ina cire hijjab da fad'in, “Cizon lips yazama maka jiki, harya zama d'abi'ar dake yawan birgeni agareka”. Lips d'in nasa ya ciza sannan ya saki wani k'asaitaccen murmushi da girgiza kai, Munaya kenan sarkin k'uruciya. Yafad'a a zuciyarsa yana mik'ewa shima. Saman sofa ya zauna yana d'aukar system ya d'ora a cinyarsa, ganin haka saina sauke tiren Dana ajiye a saman table na tura masa gabansa, nasansa akwai son d'ora k'afa, abinka da jinin mulki. Aiko saiya maida k'afafunsa duk biyu akai yana fad'in “thanks”. Bance komaiba sai murmushi dana d'anyi, na zuba abincin ina zama kusa dashi, tunda ya d'auki lap-top d'inan hanyar zamewa cin abincin yake Neman k'irk'ira, kuma saiya cishi. Nace, “to yanzu ya za'ayi? Ga abinci”. Batareda ya kalleniba yace, “Kici da nawa kawai ya wadatar”. Ni dariyama ya bani, amma na daure banyiba, “Nikam ina mamakin yanda kake k'in abinci saikace wani Khaleel”. Murmusawa yayi hankalinsa nakan aikinsa. Yace, bazaki ganebane, nifa wlhy abinci takuramin yakeyi, shiyyasa ko sau d'aya nacisa a rana ya watar dani”. Nace, “Nikam dai ban wadatuba, bud'e baki wannan bashida nauyi, nasandai gudun k'aton ciki kake kawai”. Dariya ya sanya kawai. Nima nad'an dara ina kai abincin bakinsa. ALLAH yanzu saikaga mutun nata hora kansa da yunwa wai karyayi k'iba, shikuma ALLAH ba ruwansa, idan haka yayoka ko ruwane kawai abincinka sai kayita”. Abincin ya shiga taunawa da murmushi saman fuskarsa hankalinsa nakan system d'in. Haka nacigaba da bashi abincin da janye hankalinsa da hira, yayinda yake aikinsa da saurarena, idan na murmushine ya murmusa, Wanda zaiyi magana ya amsamin a tak'aice, Wanda tuni na fahimci al'adarsace tak'aita magana yabaka a dunk'ule kawai ka fassara sauran. 'Dagowa yay fuska a marairaice, “My mata ki tausayamin hakanan cikina karya fashe”. Dariya nayi da nuna masa plate d'in daya koma empty. Ya waro idonsa waje yana shafa ciki, “Dan ALLAH da gaske kike dukni na cinye?”. Nakuma tuntsurewa da dariyar danake dannewa, “Yo dawa kukaci? Wlhy duk kai kacinye harma d'an k'arawa nayi”. “Chiii yarinyarnan kin gama dani, amma gama dariyar muguntar ai kanki zata k'are wlhy, ke zakiji nak'ara miki nauyi”. Dukda na fahimci inda ya dosa saina shareshi ina cigaba da dariyata, nama mik'e daga kusa dashi. “Humyim zaki gane kuranki ne”. Yay maganar yana cije lips. Da lokacin isha'i ma yayi shine ya jamana jam'i, ya kuma komawa kan aikinsa, ganin aikin ya d'auke dukkan hankalinsa saina d'auka wayarsa Na kira su Zuhuriyya y'an Niger, muka gaisa dad'an ta6a hirar zuminci cikeda nishad'i. Sannan Na kira aunty Salamah itama nasha labari. Ganin harna gama wayoyina yana aikin still saina d'auka Novel d'insa d'aya nai zaman karatu. Sai wajen 10 ya dafe kai yana sauke ajiyar zuciya. Kallonsa nayi da tausayawa. Nace, “Ka huta haka nan mana my king”. Huci yakuma furzarwa yana k'aramin tsaki, ya taso daga gaban tebir d'in ya dawo bakin gadon ya zauna. Hannunsa Na kamo, Na kwanto kansa bisa cinyata inad'an shata goshinsa, idonsa a lumshe yace, “wlhy sonake naga na had'a kud'in jirgi da abubuwan buk'atar mu idan zamu wuce Nigeria, Dan Dr Erfan Fahad yamin albishir da k'arshen watannan insha ALLAH zai sallami Abie, gashi ina cikin matsalar kud'i Munaya, narasa yanda zanyi, bazai yuwu Na kwashe kud'in kasuwa Na narkarba kuma”. Ajiyar zuciya Nima nayi cikin damuwa, ganin ya bud'e idonsa saina murmusa ina d'an matsa masa kafad'unsa. Nace “ga shawara to”. “Ina saurarenki”. Yafad'a cikin maida hankali gareni tareda hard'e hannayensa a k'irji. Yatsana d'aya Na d'ora saman girarsa ina kwantar da gashin a hankali, “My King mizai hana gifts d'in dana samu Na aure da haihuwar yarannan kayi amfani da kud'ad'en ciki, abinda ya kasance Na kud'i a siyar dashi Dan banga amfanin ajiyesuba ai”. 'Dan Murmushin gefen baki yayi yana lumshe ido, sannan ya bud'e a kaina, “Munaya duk abinda aka baki ko yarana halalinkine, idan Na kar6a nazama mai handama kenan, ta wani faninma zaluncine, nine yakamata Na baki domin sauke wasu nauye-nauyenki Na y'an uwa da makamantansu, saikuma Na amsa Dan nine baba rodo sarkin babakere”. Na 6ata fuska ina janye hannuna daga saman girarsa dukda dariyar da furucinsa Na k'arshe ya bani, “Shikenan tunda baka d'aukeni yanda Na d'aukeka ba, yanzu tsakani da ALLAH idan kabarni dasu mizanyi dasud'in? Ashe abuna ba naka baneba?”. Nai maganar cikin matso hawaye. Da Sauri ya tashai zaune yana rik'oni amma saina kwace ina niyyar sauka ma gaba d'aya daga gadon. Gaba d'aya yasani a jikinsa yana fad'in, “Sorry tsaya muyi magana to kinji my sweetness, ya kikeso ayi yanzun?”. Hawayen nakuma sharewa nace, “Ka kar6a kawai”. Shiru yay yana kallona da nazarin maganar, saikuma yad'an numfasa yana gyara zama. Yace, “to ai naga suna Nigeria? ”. “A'a suna nan, Dan dukna had'osu Na taho dasu wannan karon”. “Ok babu damuwa, da safe zamuyi magana, shirya yara nakaisu wajen Momma dare nayi nafara jin barci”. Naji dad'i daya amince zai kar6a, Dan haka Na rungumeshi ina dariya. Bayana yad'an bubbuga kawai yana cewa “jeki shiryasu”. 'Dagowa nayi ina kallonsa, “Amma my King zamuke takura mata itama ai, ka barsu kawai”. “Babu wani takurawa, bazaki gane bane y'ammatana”. Babu yanda Na iya, dan babu jayayya a tsakaninmu, shiryasu nayi Na shayar dasu kowanne yay d'if, ya d'auka biyu yakai yadawo ya d'auki d'ayan shima. Nikamdai wannan Abu ya girmeni, amma babu damar magana. Ya dawo yana dariya da bani labarin gargad'in da momma tamasa akan wlhy mu tashi da wuri, kokuma da anyi sallar asuba yazo ya d'aukesu, Dan bazai yuwu ake barinsu da yunwaba. Sai Na k'arajin duk kunya ta lullu6eni, amma shi ko'a kwalar rigarsa, saima wata tashar daya kamo. A gurguje please😊. ************************ Washe gari ya koma Kashmir, yaso mu tafi tare amma Na nuna masa Momma yakamata ta fara zuwa, Dan tunda aka kai Abie babu Wanda yaje saishi kad'ai. Daga baya dai sai muka tsaida shawara akan zaije yafara ganin halin da ake ciki a yanzu, da wannan shawarar yatafi. Ba k'aramin abin mamaki Dr Erfan ya shiryama Galadima ba, shiyyasa gaba d'aya ya hanashi ganin Abie. Da yamma lik'is Galadima ya isa Kashmir, saboda bai tafi da wuriba, kai tsaye asibiti ya nufa dukda yana tunanin mawuyacine ya samu Dr Erfan Fahad a can, saboda lokacin tashinsa aiki yayi, saidai idan wani muhimmin aiki ya tsaidashi ko Emergency ya riskeshi. Ilai kuwa a harabar asibitin Galadima yaci karo da Dr Erfan Fahad ya fito zai wuce gida, sosai Dr Erfan Fahad yay mamakin ganin Galadima, Dan basuyi waya yana hanyaba. Ya bashi hannu sukayi musabaha da rungume juna, “wai my friend dama kana hanya?”. Galadima ya murmusa da shafa kansa, “Kabari kawai, ya aikin?”. “Alhmdllh”. “To inaga kawai muwuce gida. Dan wlhy nagaji sosai, yau nayi aikin daya wuce kima”. Galadima yay d'an jim alamar tunani. Murmushi Dr Erfan Fahad yayi yana dafa kafad'ar Galadima, “Sameer nasan kana tsananin buk'atar son ganin Abie ko? Karka damu, kaidai muje gida kawai abokina”. Galadima baice komaiba ya bisa suka wuce, Dr Erfan Fahad nata jansa da hira, amma shi iyakarsa murmushi ko eh da a'a. Ko kad'an Dr Erfan Fahad bai damuba, danya fahimci halin Galadima Na rashin son hayaniya tsaf, dama tun a baya bashida yawan magana, Ashe halin Na nan bai canjaba, saima k'aruwa dayay. Shikam Dr Erfan Fahad mutum ne faran-faran, ko jama'ar dake jiyya namasa wannan shaidar ta yawan tsokana. Ahaka dai suka isa gida, shidai Dr Erfan Fahad yanata murmushinsa. A k'ofar falo ya tsaida Galadima, tareda fidda handkerchief a aljihunsa yace Galadima ya rufe idonsa. Da mamaki Galadima ke kallonsa, amma yagaza furta komai. Dr Erfan Fahad ya jinjina masa kai da had'e hannayensa alamar rok'o. Ruf Galadima ya rife idonsa, Dr Erfan Fahad ya saka handkerchief d'insa ya d'aure masa ido, sannan ya kama hannunsa suka shiga ciki. A tsakkiyar falon ya tsaidashi, ahankali yace, “my friend are you ready?”. Cikin sauke numfashi Galadima ya d'aga masa kai. Dr Erfan Fahad ya murmusa yana kwance masa handkerchief d'in sannan yace, “Bud'e idonka”. A hankali Galadima ya shiga bud'e idanu, harya bud'esu gaba d'aya akan k'yak'yk'yawan dattijo zaune bisa kujera, fuskarsa ta k'awatu da murmushi, yasha gyaran fuska mai k'ayatarwa, sai gashi kad'an mai adon furfura da aka bari ya zagaye fuskarsa. Wata zabura Galadima yay mai kama da firgita, Dr Erfan Fahad yay saurin tarosa, Dan kad'an yarage ya zube a k'asa. Cikin rawar baki data jiki yake kallon dattijon, dak'yar ya iya fusgo numfashi da magana mai cike da in'ina daga bakinsa “A..b..ie k..ai.ne?”. Abie ya share hawayen da shima suke ziraro masa, cikin tsantsar so da k'aunar d'an nasa yabashi amsa da fad'in “Tabbas nine Muhammad Sameer sanyin idaniya, Abie d'inka ne zaune yau agabanka, Wanda ya tashi cike da hukuncin Ubangiji gagara misali”. Galadima ya maida kallonsa ga Dr Erfan Fahad. Murmushi Dr Erfan Fahad yayi, “Karkayi kokwanto da ikon ALLAH Sameer, shike kwantar da Wanda yaso, Yakuma tasheshi a lokacin da yaso, dama ba'a yankema rayuwa hukunci, mai jiyya saiyayi rayuwa mai tsayi amma mai lafiya a wayi gari yazama gawa, ciwo bashi bane mutuwa, kwanaki 10 kacal Na d'auka ina treatment d'in Abie ga66ansa suka fara aiki, a sauran sati uku danayi tare dashi muna koya masa yanda zaiyi tafiyane, da zama, d'aukar Abu, da sauransu, Dan duk ga66ansa sun manta, kamar yanda ka sanarmin addu'ar da kukaita masa lallai itace babban magani daya zama mai tasiri a garesa, domin nikam abinda ba'a rasaba Na k'arasa, duk Wanda yabar addu'a lallai dole matsala tazama ma'abociyar rayuwarsa, a yanzu haka ina mai tabbatar maka Abie zai iya tafiya dayima kansa wasu abubuwa, amma bamasu yawaba, tafiyarma bamai tsaho ba, Dan yawanyin ne zai bama ga66ansa kwari da sabo, shekara 26 mutun Na kwance sai na'urori ke sarrafashi ba k'aramin Abu bane Sameer, Dan dolene akira Abie d'an baiwa, masu irin nasarorinsa kad'anne a cikin al'umma wlhy, kaje ga Abie, domin kuna buk'atar juna”. Tamkar Dr Erfan Fahad yama Galadima allura ne, cikeda sasaarfa ya k'arasa ga Abie, a gabansa ya zube yana sakin wani kuka maiban tausayi tamkar mace”. Abie ya sakko daga kujerar ya rungume jarumin d'ansa shima yana hawaye, sun dad'e a haka, jisuke tamkar karsu saki juna, a tunaninsu Kodai mafarki sukeyi, suna tsoron rabuwa su farka suga ba haka baneba. Shi kansa Dr Erfan Fahad hawayen tausayinsu yake sharewa. Ni kaina masu karatu wannan lamari yasani hawaye Na gaske😭, da zaka k'iyasta hakan a kanka wane farinciki kake hangowa yayinda waraka ta riskeka?.😭 Wad'annan bayin ALLAH yau lallai suna cikin tsantsar farin ciki, ko kad'an Galadima ya kasa gusawa daga jikin Abie, Yakuma k'i kiran kowa, burinsa shima yabasu mamaki tamkar yanda Dr Erfan Fahad yabashi. A yau yay niyyar su juya amma Dr Erfan Fahad ya hana hakan saidai gobe, Dan dare yayi kam a yau. A gado d'aya Galadima da Abie suka kwana, dukda sunma cinye rabin daren da fira😁. ********** Hankalin Munaya duk a tashe yake, saboda tanata kiran Galadima yak'iyin picking, tun tana daurewa harta gaza tafara kuka da shiga tsantsar tashin hankali. Momma Ce ta lura da canjawarta, ta tambayeta lafiya?. Kasa magana tayi saboda kunya, saida Momma ta kuma maimaitawa sannan tace, “Momma inata kiran Number Abbansu ne yak'i yin picking tun d'azun”. Ita kanta Momma ta kirashi baiyi picking ba, amma ta d'auka ko wani uzirine yasha kansa, sai yanzumefa hankalinta ya fara tashi itama, waya ta d'auka tashiga kiransa amma babu amsa, kusan kira 10. Cikin firgici ta kalli Munaya da aunty Mimi da itama take kan gwada kiran nasa, amma itama ba'ayi picking. “Kinga Munaya tura masa massage mu gani”. Jiki a sanyaye Munaya ta tura massege, amma kusan 30minutes babu reply. Hankalinsu fa yakai k'ololuwar tashi, amma sun rasa mafita. ********* Shikam Galadima baima San sunaiba, wayarma kanta baisan inane ya jefar da itaba, gabaki d'aya hankalinsa ya tattarane ga Abie, harkuma suka kwanta barci bai nemi wayarba. *********** Yau kam inhar wani yay barci a cikinsu to bana kwanciyar hankali baneba, dan kowa damuwa tamasa katutu, dai-dai da Hadiman gidan suma duk a damuwa suke, sai dai tamkar yanda suka saba yauma sun mik'a lamarinsu ga Ubangijin talikai. *_Washe gari_* Tunda safe Momma ta nemi Number Dr Akash da Dr Ajey akan rashin jin Galadima, duk sun amsa mata da zasu bincika. Can kuma su Galadima sun wayi garine da shirin dawowa New Dhalhi, cikin tsantsar farin ciki irin Wanda misaltashi ma 6ata lokacine.................✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [8/21, 8:44 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻2⃣9⃣ .................Gaba d'aya sun kasa yin breakfast, suna cikin zaman jigum-jigum suka jiyo bud'e gate da shigowar mota. Samha ta fita da hanzarinta danson ganin wanene, fitowar tata tayi dai-dai da fitowar Galadima daga cikin mota fuskarsa d'auke da wani irin k'ayataccen murmushi daya fidda sirrin k'yawunsa. Da gudu ta taho garesa, yakan mata fad'a akan son rungumarsa ko Sauban amma yau saigashi ya bud'e mata hannu dakansa tazo ta shige jikinsa. Ihun murnartace tasaka su Momma fitowa da hanzari suma Ganin Galadima ai sai duk sukayo kansa itada aunty Mimi, itadai munaya gefe ta tsaya tana sharar hawayen farin ciki. Abie dake kallonsu daga cikin mota ya saki murmushi yana share hawaye, yana k'asa d'aya da iyalansa amma bai ta6a sanin muhallinsu ba sai yau, dukda bai shigaba gidan yamasa k'yau. Galadima ya ture Samha daga jikinsa ya rungume Momma da aunty Mimi yana sakin wani irin kuka daya matuk'ar tada hankalinsu. Da sauri suka d'agosa hankali tashe suna tambayarsa mike faruwa? Kodai ALLAH yayima Abie rasuwane?. Cikin kuka da dariya yace kowa ya rufe idonsa . Babu musu sukabi Umarninsa, har Munaya dake gefe. Yace, “kun tabbatar kowa ya rufe?”. A tare suka amsa masa da eh. Ya murmusa da goge sauran hawayensa sannan ya juya ga motar ya bud'e, hannun Abie ya kama da taimakonsa ya fito rik'eda sandarsa mai k'yau dazata dinga taimaka masa wajen tafiya, Dan har yanzu tafiyar batai kwariba. Saida Abie ya jingina jikin Mota ya tsaya da k'yau sannan Galadima yace, “Kowa ya bud'e idonsa”. Har rige-rigen bud'ewa suke. Akusan tare Aunty Mimi da Munaya da Samba suka kwalla k'ara, Momma kam sai tayi luuu sai gata a k'asa kawai ta sume. Abie da Galadima dasu Munaya duk kanta sukai suna kiran sunanta, shima Abie ya tuzgud'e zai fad'i, Dr Ajay daya kawosu yay hanzari rik'esa yana fad'in “A sannu dai Sir, k'afafunka basukai k'warin wannan hanzarinba”. Da gudu Munaya takoma ciki sai gata da ruwa, ta zuba a hannu tana shafama Momma, da k'arfi takawo Numfashi. Bin yaran nata tayi da kallo tana fad'in “mafarki nakeyi ko yarana? Nasan irin mafarkin dana sabane dama, ba takawa Na bane ba”. Cikin dariya da kuka Aunty Mimi tace, “Wlhy shine Momma, shine agabanki ba mafarki kikeba, Momma Abie d'inmune wlhy tallahi kinji Na rantse”. Zumbur Momma ta tashi daga jikin Aunty Mimi, Abie dake tsaye har yanzu bisa taimakon su Galadima ya murmusa yana fad'in “Zeenah ki cire kokwanto, da gaske wannan Saifudden d'inkine ba Wanda yasaba zuwa miki a mafarkiba kinji”. Tasowa Momma tayi garesa, ta shafa fuskarsa domin tabbatarwa, takuma binsa da kallo tundaga sama har k'asa, lallai da gaske wannan Saifudden d'intane bana mafarkiba, Ai sai kawai ta rungumeshi babu kunya ko tunawa dasu Galadima a wajen. Sai duk'ar da Kansu duk sukai suna Murmushi. Gaba d'ayansu kowanne soyake ya nuna ajintarsa ga Abie domin nuna masa gamsuwa da farincikin samun lafiyarsa, aka kawo masa y'an Uku ya had'a duka ya rungume yana maijin k'aunarsu har cikin jininsa, Khaleel ma yana nanik'e dashi. Munaya dai nadaga gefe bata zak'eba. Idon Abie ya sauka akanta, Murmushi yamata yana fad'in “'Diyata zo mana”. Takowa tai cikeda jin kunya tazo gabansa ta durk'usa, cikin girmamawa ta gaisheshi da masa addu'ar k'arin samun lafiya mai d'orewa. Ya amsa yana mai k'ara jin farin cikin kadancewarta suruka agaresa uwa ga jikokinsa. Galadima ma yakasa d'auke ido daga gareta, sai yaga tamasa y'ar rama tsakanin jiya da yau. Breakfast d'in dabai samu shigaba d'azun aka baje domin ci, amma shi Abie kasancewar an hanashi cin wasu Abubuwan Kuku yay azamar tanada masa Wanda yake buk'ata. Daka gansu kasan suna tareda matsanancin farin ciki . Koda suka kammala Galadima ya taimakawa Abie shiga d'akin Momma, shima ya haye sama shida matarsa. Tun'a falo ya d'auketa cak yana juyi da ita cikin hajijiya, babu shiri Munaya tahau k'yalk'yata dariya da k'an k'ame wuyansa da hannayensa tana cusa kanta cikin k'irjinsa. A haka suka k'arasa cikin bedroom, ya jefa abarsa saman gado yabita tareda jan bargo yay musu runfa. An hanani ganin abinda akeyi🤨, sauk'inma inada mijin Nima😏🙄. Farin cikin da wannan ahali suka tsinci Kansu wlhy 6ata lokacine, Momma kam sai ko ganinta bama ayi🤭🙈. A gurguke please🥺😔. Walwala da farin cikin wannan gida tadawo kam, ga nutsuwa mai saka zukata samun damar yawan ibada, ko yaushe suna manne da Abie, sai idan time d'in hutunsa ne yayi, Galadima yayma kowa gargad'i akan sanarda tashin Abie, burinsa kowa yaga abin mamaki, 100% Momma ta yarda da shawararsa, hakama Abie. Yanzu dai kam sun yanke shawarar Isa k'asarsu ta haihuwa ranar salla k'arama, zasu azumi na kwanaki 20 a india, su biya Saudiyya suyi Umrah ta kwana goma su isa Nigeria a ranar salla ayi idi dasu. Gaba d'aya azumi saura kwanaki 6 a farashi. ****************** *_AZUMI_* Alhmdllh kowanne musulmi yau ya tashi da azumin watan Ramadan mai mai albarka, saidai irin masu ak'idar saimun gani da suka kasance k'alilan acikin wasu k'asashe irin namu Na yankin Africa. Duk da shayarwa hakan bai hana ni zama cikin jerin masuyiba, dan raino dai bani nakeba, tsakanina da yarannan idan sunji yunwa, koyaushe suna tare dasu Momma, sunyi 6ul-6ul dasu tamkar y'an watanni 6, amma har yanzu suna cikin wata Na hud'une ma kacal. Tunda safe Galadima ya fice, Na d'an tashi nai gyaran saman sannan Na sakko, yau babu maganar shiga kitchen, Dan tunda Abie ya dawo nakoma nike mishi girkin abinda zaici, wataranma nakan had'a da namu muma, babu abinda zan cema wad'annan mutane sai godiya, soyayya dai mai cike da k'auna ina samunta a garesu, ni da mijina kam ai sai hamdala, yana tattalina da tarairayata, saidai d'an sa6ani Na yau da gobe Wanda baka Isa raba ma'autara da Shiba, shima kuwa bai wuce wasu awanni muke shiryawa ba, inko Momma ta lura ma takan kiramu tamana Nasiha, hakama Aunty Mimi. A falo Na iske Abie daga can gefen falon inda wasu kujeru biyu suke da kanta mai d'aukeda buks Na karatu, tundaga kan Na addini har zuwa Na makaranta dadai sauransu, zaune yake yana nazarin wani littafi da banga sunansa ba saboda tazarar dake a tsakaninmu. Sai Samha dake falon kwance a kujera tana kallon film, zaman gyalena Na gyara, Na taka a nutse zuwa garesa, saida Na durk'usa a gabansa sanann nace “Barka da safiya Abie”. 'Dago k'yawawan idanunsa da Galadima ya gado yay yana kallona, ya zare medical eyeglasses d'in idonsa yana Murmushi, “'Diyata barka dai, kin tashi lafiya?”. Kaina a k'asa ina murnushi nace, “Lafiya lau Abie, ya ibada da k'arin k'arfin jiki?”. “Alhmdllh d'iyata, ai jiki kam sai godiyar Ubangiji, Muhammad fa?”. “Ya fita tunda safe”. Na fad'a cikin kuma duk'ar dakai. Murmushi Abie yayi, ya maida eyeglasses d'insa yana fad'in “ALLAH ya dawo dashi lafiya to”. A saman la66a Na amsa, sannan Na mik'e da k'yar zuwa d'akin Momma. Abie ya bita kallo zuciyarsa cikeda k'aunar wannan yarinya, irinta yaytama y'ay'ansa addu'ar samu amatsayin abokiyar rayuwa, Alhmdlh Ubangiji ya amsa masa, saura Sauban kuma. Nidai nashiga Na gaida Momma, Na iske tanama su Amaturrahman shiri, da alama wanka tamusu, Na gaisheta cikeda girmamawa kamar yanda Na saba, itama ta amsamin da kulawa tareda d'an jana da hira tamkar yanda ta saba, nad'an jima a d'akin, harta fito tabarni Na gyarashi tsaf kamar yanda nakeyi tun bayan dawowarmu, Dan tuni Na dakatar da Samha ni nakeyi. Na fito da nufin shiga Na gaida aunty Mimi saina isketa tama fito falo, anan muka gaisa Na zauna muka d'ora da hira tamkar yanda muka saba, mafi yawama firar ta Sauban Ce, Dan kowa yayi missing d'insa, yace azumi da kwana 3 zai zo sai salla zai koma, Galadima bai hanashiba, dukda yana tareda tattalar kud'i a tsakaninnan saboda sun masa k'aranci, to saima papi ya d'auki nauyin zuwan Na Sauban da komawarsa. Mund'an ja lokaci Muna hira barci yafara rinjayata, mik'ewa nayi Na gudu sama, nad'an rage kayan jikina Na haye gado sai barci. Kusan 10am saiga Galadima ya dawo, bai iske kowa a falonba, da alama barci suke kokuma suna harkokin gabansu a ciki, kai tsaye d'akin su Momma ya nufa, yay knocking aka bashi izinin shiga. Abie Na zaune saman abin salla ya idar da sallar walha, yayinda Momma ke zaune bakin gado tana bama Abdurraheem Magani saboda zazza6in dake jikinsa. Galadima ya zauna a saman sofa yana gaidata da tambayar miya sami Abdurraheem d'in?. Cikeda kulawa ta amsa masa tana gogema yaron inda maganin ya 6ata masa a wuya da fuska. “Tunda muka tashi yau Na kula bayajin dad'i yaronnan, inagafa yakamata ka kaishi a bincikasa, basai mun zauna wata 6 ta cikaba, tunda kasan ciwon yana zama iri daban-daban, karmuyi tunanin ko irin nakane azo ba hakaba, Dan Na kula yafika yawan laulayi shikam, Abdurraheem baya had'a sati biyu da isashsshiyar lafiya”. Jin jina kai Galadima yayi, tausayin d'an nasa Na ratsashi, ya had'iye abinda ya tsaya masa a mak'oshi da k'yar yana amsar Abdurraheem d'in daga hannunta. Abie daya shafa addu'a ya maido hankali garesu. Mik'ewa Galadima yay yakoma inda yake yana gaisheshi, Abie ya shafa kansa hakama Abdurraheem, cikeda tsokana yace, “Like Father like son”. Dariya Momma tayi, yayinda Galadima yay Murmushi mai k'ayatarwa har hak'oransa Na bayyana. Yace, “Abie ai dakai suke kama duka, Amaturahman cema tad'an d'ebo mamansu kad'an”. [8/19, 6:14 PM] 🙇🏻‍♀Da Rarrafe🙇🏻‍♀: Abie yay Murmushin jin dad'i, yana shafa kan Abdurraheem da yay barci, gaskiya Galadima ya fad'a, dan shima tun randa yafara ganinsu ya lura da haka. Sund'an ta6a hira, har Galadima ke kawo maganar Aunty Mimi akan yakamata tayi aure hakanan, domin zaman bashida amfani haka, ko wani yamaka k'yak'yk'yawar fahimta wani bazai makaba, tunda ba wuce auren tayiba. 100% iyayensa sun gamsu da zancensa, sunkuma amsa masa da isha ALLAH zasu zama Na musamman da ita. Kwantar da Abdurraheem yay musu sallama akan zaije yad'an rage barci. Tunda ya shigo yay tozali da Munaya barbaje a gado, murmushi yad'anyi yana cire Bottoms d'in rigarsa harya k'araso cikin d'akin, hanging d'in rigar yay sannan ya zauna saman sofa yana cire takalmansa, mitsawar da Munaya tayi tana juya kwanciya yad'ago ya kalleta, aransa yace hajiyata ko an farajin azuminne?. Harya gama hidimarsa yazo gefenta ya kwanta bata saniba, dayake ba motsi mai k'arfi yay tayiba, Dan yasan batada nauyin barci, gudun karta tashi yay tayin komai a sannu. *********** Duk musulmin ALLAH Na k'warai daya wadatu da ibada inhar lokacin salla tayi ko barci yake saiyaji a jikinsa, kokuma yayta mafarkin ana sallar, hakance ta kasance ga Munaya da Galadima, kusan atare suka farka, kowanne bakinsa d'auke da addu'ar tashi barci. mamaki ya kamani ganinsa gefena, Dan bansan yama dawoba, ya min murmushi nima Na mayar masa da murtani ina shafa fuskarsa. Cikin lumshe ido nace, “Yaushe ka dawo?”. Hannunsa ya d'ora saman nawa dake kan fuskarsa, yad'an rufe ido ya bud'e akaina, murya k'asa-k'asa yace, “Tun d'azun mana, kinata barci abinki”. Yatsine fuska nad'anyi ina zame hannuna da k'ok'arin tashi. Nace, “Wlhy barci bai wani isheniba shiyyasa nad'an rage yanzu kafin time d'in shiga kitchen”. Shima tashi yay zaune yana jinjinamin kai. Shiya fara shiga wanka, saida ya fito sannan nima Na shiga nayo. Koda ya fita salla ya dawo bai koma cikiba, sai suka zauna a harabar gidan shi da Abie suna hira, dayake kullum Galadima cikin bashi labarin abubuwan da suka dingi faruwa yay lokacin yana jiyya, wani yay murmushi, wani dariya, wani kuka, yana kuma yabama Galadima bisa ga gwarzan takar dayayi ta kare mutuncin ahalinsa da rik'e martabarsa. Har time la'asar suna zaune a wajen, da taimakon Galadima Abie yataka zuwa massalaci, dan inhar yana gida haka sukeyi, bayan sun dawo awajen suka sake zama, Galadima ya kirani nabama Samha System d'insa takai masa. Da to Na amsa, Na hau sama Na d'akko nabata. K'arfe biyar dai-dai muka shiga kitchen ni da Samha da kuku, sai Hadiman gidan guda biyu dake taimaka mana da wasu ayyukan. Cikin nutsuwa muka gabatar da dad'ad'an abincin bud'a baki, wasu namu Na Hausa wasu kuma Nan. Gab da magrib muka gama, munbarsu k'arasa komai Na k'imtsa kitchen d'in da shirya abincin. Wanka nakesonyi ga Amaturrahman Na kuka, Momma kuma tace babu inda zani saina shayar da ita. Dole Na zauna ina dungure kanta. Oho batasan ma inayiba, itadai taji abinda take buk'ata a baki kawai. Ganin tad'ansha na d'auketa muka haye sama dan karma Momma tace saita k'ara. Na iske Galadima yana wanka, ni bammasan ya shigo cikiba, Na kwantar da Amaturrahman Na kuma sauka, nasan dole yana d'akin za'a kira salla, dabino da ruwa Na d'oro a k'aramin tire nazo Na ajiye, ina ajewa kuwa yana fitowa. Sannu da aiki yamin, Na amsa ina manna masa Sumba a hannunsa dana kama, nai saurin shigewa bathroom. da kallo ya bita yana murmushi, ya kalla hannunsa data sumbata shima ya sumbaci wajen. Fitowata wanka yay dai-dai da cikar lokacin kiran sallar magrib, a bakin gado Na iskesa zaune Amaturrahman Na kwance kusa dashi tana wuntsil-wutsil da k'afafu, idonta nakan hasken globe, shikuma yana kallonta yana murmushi da video d'inta awaya. Batare danayi tunanin komaiba Na k'araso garesa da nufin bashi dabinon, amma saiya jawoni nafad'o jikinsa, dukda laimar ruwan dake jikina. Babu wani k'arin bayani ya d'aura bakinsa saman la66ana, idanu Na waro masa Na tsorata da mamaki, amma saiya kashemin ido d'aya da cigaba da abinda yake. Kusan mintuna biyu nasamu ku6ta. Ina yunk'urin tashi ya kuma hanani. “O ALLAH, azumi fa kakai my King, shine kafara da jan magana mai makon Neman ruwa ko dabino?”. Wani miskilin murmushi yayi da huramin iska saman ido. Farfar Na fara da idanu. Yakuma Murmusawa, “Bazaki ganeba babie na nayi missing d'inkine, kinga ai lada biyu, gatakai azumi gata d'abbak'a sunna, ni ai ga dabino Na nan, yawunki kuma shine ruwana”. Ya k'are maganar yatsansa a la66ana. Tura kaina nayi a jikinsa ina Murmushi. Ya rungumeni da shafa bayana shima yana murmushin. K'arshe dai sai a d'akin mukai sallar magrib sannan muka sauka k'asa shan ruwa. Jinai gaba d'aya kewar y'an gidanmu tazomin a yau, Na tuna yanda muke had'uwa k'wanmu da kwarkwata a runfa shan ruwa, murmushi naita saki dajin kewarsu mai yawa da d'okin son ganinsu. Aunty Mimi data lura dani tace, “My K'anwa yadai?”. Nakuma fad'ad'a fara'ata ina cewa “Na tuno gidane kawai Aunty”. Murmushi duk sukayi, Galadima dake gefena ya mintsini cinyata kad'an, d'agowa nai Na kallesa ina d'an 6ata fuska, gwalo yay min kad'an yana d'auke kai cikeda basarwa tamkar bashi yayiba. Saida na tabbatar bamai kallonmu sannan nima na rama, aiko zafin yasakashi kad'an garage ya 6arar da kunun da yake sha, yay saurin rik'ewa. Sannu muka shiga masa, na Fiske abina tamkar banyi komaiba. Muna had'a ido ya cije lips da min gargad'i da ido akan zai kamanine. Nima gwalo namasa. Abinda basu saniba tun farkon fara lamarin Abie da Momma suna kallonsu, dan haka yanzu sai suka kalli juna suna murmushi. A gurguje please⛹🏻‍♀😏 ★★★★★★★★★ Kwan uku da fara azumi Sauban ya iso India, bak'aramar birkicewa yay da ihun ganin Abie ya samu lafiyaba, hardasu kuka rurus, Abie ya rungume Autansa d'aya zama sangamemen Saurayi yana mai jin farin ciki da k'aunarsa. A ranar sai sabuwar murna ta tashi kuma, haka muka wuni cikin farinciki biyu, na zuwan Sauban da gimama farincikin daya riska. Haka azumi yacigaba da gangarawa, kullum saina kira su Abbanmu da sauran jama'ar gidanmu namusu barka da shan ruwa, hakama y'an uwana sunta turomin sak'on massages kenan kulum namin barka da shan ruwa. Azumi na kwana 15 muka kai Abdurraheem Asibiti, Yakuma samun binciken kwararrun Likitocin zuciya, suka dubashi da k'aramin dabaru wajen kula da rainonsa, sai magunguna da zai iya sha a matsayinsa na yaro k'arami. Dukkan sayayya da Galadima zaiyi ya kammalata, harma ya tura mana kayanmu ta jirgin ruwa. A kwanakin bashida wani sukuni, yawan shigi da fici na damk'a amanar harkokinsa kawai yake ga mutane, dan zai jima a 9ja bai dawoba a yanda ya hasaso, inma ya shigo India bazai dinga wuce sati biyu zuwa uku ba zai barta, shima saboda Company nasune, danma yanata k'ok'arin ganin sunzo sun kafa reshe a Nigeria dan shima yabada gunmawa ga k'asarsa. Muma dake cikin gidan bawani zaman mukeba, munata kimtse-kimtsen kayan gidan waje d'ayane. Da sallama da mak'wafta da abokan arzik'i da akai sabo. A wannan yanayinne na gane Ashe yayan Dhibya Gopal soyayya suke da Samha, wannan ne kusancin dake k'ara k'arfi tsakanin Dhinya da Samha, ban sanarma kowaba, haka itama ban mata maganaba, tunda gashi ALLAH ya kawo sanadin da zasu nisanci juna cikin sauk'i, babu yanda za'ayi aure ya iya yuwuwa a tsakaninsu, yaudarar juna kawai sukeyi, Su Dhibya y'an k'abilar Hindu ne, kuma mabiya wannan addini masu tsananin ak'ida, Galadima ya ta6a sanarmin iyayensu sun dad'e basu saki jiki dasuba saboda kasancewarsu musulmai kawai, Gopal kusan sa'anni suke dashi amma babu wata shak'uwa tsakaninsu. To tayaya suke tunanin k'ulluwar aure a tsakaninsu inba Gopal musulunta zaiyiba, hakan kuma abune mai wuyar gaske, dukda ba'a yanke hujunci da ikon ALLAH. Ana gobe zamu wuce saudia Galadima ya sallami Khumar da kuku, wad'anda suke kuka da idanunsu na bak'in cikin rabuwa damu, muma kuma hakanne, sai da Galadima yamusu bayani akan badan shima bayason rayuwa dasu ya sallamesuba, sai dan karya tauye hak'insune, yabasu Dama suje su nemi wasu ayyukan, duk sanda ya shigo k'asar zai nemesu su dawo kan aikinsu insha ALLAH. Sunyi murna sosai da bayaninsa, haka muma munji dad'in hakan, domin kuwa dai ba'a rabuba kenan. *_KOMAI YAY FARKO...😭👎🏻_* Zai iya zama k'arshe watan watarana, yau ga Abie daya shigo India cikin tsananin ciwo da fidda rai daga rayuwa zai barta cikin farin ciki da k'warin gwiwar rahma da falalar ubangijin al'arshi. Fuskokinmu kawai sun isa shaida maka muna cikin farin ciki muma. Mun tafi cikin kewar India da jama'ar cikinta, musamman ma Momma da Abie da tunda suka shigota sai yaune zasu barta. Tunkan mu Isa Galadima ya sanya Sultan nema mana masauki. Muna sauka kuwa cikin mutunci akazo aka d'aukemu zuwa matsakaicin gida dazai d'aukemu babu wata takura. Har kuka saida nayi a 6oye ganina a inda ban ta6a zato ko tsammaniba, kasa mai tsarki. Hutun wannan ranar kawai muka samu, washe gari muka duk'ufa ibada da godiyar Ubangiji bisa ga ni'imomi dayay mana badan munfi sauran bayinsa da komaiba. Tsawon kwana goma muna bautar Ubangiji, a randa ake saran ganin wata jirginmu ya d'aga zuwa k'asarmu ta haihuwa, Abie da Momma sunfi kowa zumud'i da k'aguwa. Babu wanda yasan da zuwanmu sai Sarkin Mota, shima kuma bashi da tabbacin dawa za'azo d'in, Galadima dai yace ya saka a gyara masa 6angarensa da inda su Aunty Mimi ke sauka. *************** Jirginmu ya sauka 9ja k'arfe 11:30pm. Mu muka fara fitowa, Abie da Galadima suka zama k'arshe. Abie na sauka a jirgin yana Murmushi da hawaye, tareda shak'ar iskar k'asarsa daya bari tsawon shekaru, yama fidda ransa da kuma dawowa cikinta har Abadan. Sarkin Mota da dogaran Galadima suna zaune a airport d'in suna jiran isowarmu. Ganinmu da yawa yabasu mamaki, amma saisuka zube suna gaishemu, a cikinsu babu Wanda ya gane momma da Abie, Bama zai yuwu su ganesu d'inba, tunda sanda yabar k'arsar duk basa a wannan matsayin, sai dai iyayensu, wanda a halin yanzu mafi yawa acikinsu duksun rasu ma. Dole saida muka k'ara da motocin haya, Momma da Abie suka shiga wadda sarkin Mota ke ja, Ni da Galadima da Samha muka shiga ta haya d'aya, Aunty Mimi da Yaa Sauban da yara suka shiga d'aya. Mun Isa Masarautar tsit babu yawan hayaniya alamar mafi yawan al'ummar cikinta sun nutsu waje d'aya, sai wasu tsirarun hadimai dake kai kawo mussamman masu tsaro. Duk muka fito amma banda su Momma, Galadima ya nufi mortar dan son taimakawa Abie fiwo, Sarkin Mota kuma na k'ok'arin biyan masu motarnan kud'insu. Fir Abie yak'i fita, yace d'an uwansa mai martaba ne kad'ai zai fiddashi a motar, duk rok'on da sukai masa fir yak'i, gashi yanata sharar hawaye da handkerchief. Galadima yasan yanzu Mai martaba ya shiga ciki, maybe ma matar dake dashi taje. Rasa yama zaiyi yayi. Momma Ce tabashi shawarar kiran wayar mai martaba, cikin damuwa Galadima ya kar6a wayan Sauban dabe dad'e da barin k'asarba, sim card d'insa zaifi saurin aiki fiye da nashi. Hadiman gidan sund'an fara fuskantar akwai matsala gameda tsayuwar su Galadima, dan wannan ba halinsa bane. ALLAH ma ya taimaka Mai martaba baiyi barciba, yana zaune ne yana duba wasu takardu, matarsa ta biyu na tare dashi dan yau kwanantane. Ya dad'e yana kallon wayar da nazarin mai kiransa, dan ba kowane keda Number mai martaba, sai jiga-jigai irinsu Galadima d'in. Tamkar bazai d'aukaba yad'ai d'auka tana gab da katsewa a kira karo na biyu. Cikeda girmamawa Galadima ya gaishesa sanann yay masa bayanin shine. Da farko mai martaba tsorata yayi, dan babu Wanda yasanar masa Galadima ya dawo, cikin hikima da girmamawa Galadima yayma mai martaba bayanin yafito yaga abin mamaki a k'ofar sashensa. Sosai mai martaba yayta juya kalmar abin mamakin, hakama matarsa, alk'yabba ta d'akko masa ya saka sannan suka fito a tare. Jakadiya na niyyar tafiya makwancinta taci karo da mota a k'ofar turakar mai martaba, mamaki ya kamata, zatayi magana saitaga Galadima dake tsaye a jikin motor, ta rusuna tana gaisheshi, kamar yanda yasaba ya d'aga mata hannu cikeda izzar mulki. Bata fita a mamakinba taga mai martaba da matarsa sun fito. Galadima baice komaiba sai bud'e murfin motar da yay yana nunama mai martaba ciki da hannu. Jikin baiwar mama Fulani mai kai mata rahoton motsin kowa na rawa ta nufi sashenta, hartayi shirin barci ma ta sallami Kuyanginta, amma dayake baiwar tanada fada sosai a wajen ta saita mata knocking k'ofa. Cikeda masifa da izza mama Fulani ta bud'e k'ofar, jikin baiwarnan na rawa ta zube k'asa tana fad'in “Ki gafarceni ranki ya dad'e, abinda nagano yafi k'arfin barinsa zuwa safiya, yalla6ai Galadima ya shigo fada shida sauran iyalan tsohon sarki, maimakon yawuce sashensa tamkar yanda ya saba saiya nufi turakar mai martaba kai tsaye, gashi can naga yana nuna masa Abu amota, ban tsaya ganiba na nufo gareki ya uwar gijiyata”. Ai mama Fulani bata tsaya bata amsaba ta figi alk'yabba ta saka tana fitowa, baiwarnan ta take mata baya. A can kuwa Mai martaba da mamaki ya kalli Galadima, amma sai Galadima ya girgiza masa kai yana sake nuna masa cikin motar. Matsawa mai martaba yayi sosai domin ganema idonsa abinda d'an d'an uwansa keson ya gani, Momma ta kunna fitilar dake motar dukda haske mai k'ayatarwa daya haske ko ina na masarautar. Koda mai martaba ya lek'a saiyay baya a zabure, cikin rawar baki da nuna motar yace, “Sameer yaushe kuma ka fara shirya min wasa da hankali har irin haka?”. “Ka gafarceni ranka ya dad'e, abinda kagani zahirin gaskiyane, wannan d'an uwankane ya dawo gareka cikin k'oshin lafiya da hukuntawar Ubangiji”. Galadima ya k'are maganar da rank'wafawa ya taimakama Abie ya fito, itama Momma ta fito. Hakan sai yayi dai-dai da isowar mama Fulani wajan. Da fuskar Momma mai d'auke da k'asaitaccen murmushi tafara tozali, ta k'araso gabanta da sassarfa tana rik'o hanunta da fad'in “Zeenah!”. A take Momma ta juya gareta, dan ko a mafarki bazata manta mai wannan muryarba, batareda tunanin komaiba ta rungumeta. Yayinda shima takawa ya rungume Abie daga can. Tun a wannan daren labari yafara karad'e masarautar, wasu kan basu aminceba kwata-kwata, burin kowa gari ya waye yayi kallon zahiri ba jita-jita ba. Dole matar mai martaba ta koma sashenta, dan mai martaba yace Abie a sashensa zai kwana, jiyake idan ya barsa zuwa wani sashe tamkar da safe zai wayi gari yaga ba hakaba. Itama Momma a sashen mama Fulani ta kwana tilas, yayi da mukuma muka nufi namu da yasha gyara ko ina yake need tamkar muna k'asar. Yau dai kam na murzu wajen Galadima, acewarsa murnar sallah ce, dukda gajiyar tafiya darashin samun isashen barcin da muka tara a Saudia bai d'agan k'afaba, a cewarsa yamayi k'ok'ari, kwana nawa. *_WASHE GARI_* A Washe gari antashi da farin ciki guda biyu a masarautar gagara badau, Murnar Salla da dawowar Abie. Dan zuwa safiya kam tabbataccen labari daga bakin sank'ira ya isa kunnen kowa, harma da k'yak'yk'yawan albishir na halattar sallar idi tareda Abie. Kafin kace mi labari yafara fita wajen masarautar, su papi ma tun a Daren Galadima ya kirasu da wayar Sauban dake hannunsa. Batareda sanin ya akayiba saiga magana tafara shiga kunnuwan jama'ar gari da y'an jarida, wasu gidajen TV Dana redio suka fara sanar da wannan zance dawasu ke k'arya tawa kansu tsaye................✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼 [8/21, 8:44 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _____________________ *_Tawan miss xoxo tawa ni kad'ai, wannan gaisuwar takice ke kad'ai da babbar murya my dear, ALLAH ya bar mana zuminci mai d'orewa har Abadan, ke ta dabance a zuciyar bilyn Abdull, ina yinki irin Trillion's d'innan wlhy, na gaisheki da gaba d'ayan ahalinki da tawagar y'an Group d'inki na HOME OF NOVELS baki d'ayansu, alkairin ALLAH yakai gareku har gadon barci My Hafsy🤸🏻‍♀😘👍🏻._* _______________________ *_BOOK 3_* 👉🏻3⃣0⃣ ...............Da asubahi na tashi jikina cike da gajiyar tafiya da wadda boss ya k'aramin, daga sallar asubahi bai samu dawoba, Dan ana fitowa salla dukan ahalin gidan mai ruwa da tsaki sun hallara ne ga yima Abie barka da zuwa dakuma tabbatar da gaskiyar zancen, domin tabbatar musu da kokwantonsu mai martaba yabasu damar ganin Abie d'in tareda shelar Sank'ira. Wannane dalilin yad'uwar zancen dawowar ta Abie har a wajen masarauta. Dukda gajiyar dake tare dani bansamu komawa barciba, nashiga k'imtsa gidan iya bedrooms d'inmu zuwa nashi sashen da babu wata baiwa dakeda lasisin shiga. Sauran guraren zuwa kitchen kuma bayina dasukayo asubancin zuwa sashen saboda jin nadawo ne keta k'ok'arin gyarawa. Na fito da nufin komawa d'akina na tashi yara na musu wanka cikin bayina d'aya ta zube Guywoyinta a k'asa tana fad'in “Ranki ya dad'e ga sak'on kayan abincin salla nan daga sashen mama fulani”. Cikin d'an mamaki Na kalleta tareda kayan abincin dake jibge, sai naman kaji cikeda k'atuwar roba irin wadda ake tarama mai jego ruwan wanka. Katsemin tunani tayi da kuma fad'in, “Ki gafarceni ranki ya dad'e, wannan al'adar mama Fulani Ce, a duk daren salla takan aikama kowanne sashe Na y'ay'anta da manyan gidannan irin wannan kayan, yanzu zama a k'araso da sauran, kowane sashe dasu yake abincin salla”. Kaina Na jinjina tareda zama bisa kujera ina d'ora k'afa d'aya kan d'aya da kallon baiwar dani nama mance sunanta a yanzu. Nace, “Oh, yama sunanki?”. “Ranki ya dad'e Umimi”. “To Umimi wace shugabar hadiman sashen nan?”. “Nice rankai ya dad'e”. “Ok, ya zamuyi kenan? gashi mun kasance lokacj a k'ure, Dan yanzun kinga kusan 6:23am, bamuda isashen lokacin abincin salla kenan”. “Ranki yadad'e ki gafarceni, zamu iyayi insha ALLAH, tunda kinga ai munada yawa”. Shiru nayi inad'an nazari, saikuma Na sauke numfashi ina mik'ewa damata nuni muje kitchen d'in. Alhmdllh inada kaso mafi yawa Na buk'ata, saidai abinda ba'a rasaba, Umimi nasaka ta tattaro sauran suka shigo da kayan, Dan danan suka fara rage aikin, ni kuma Na fito nad'an rubuta sauran abinda nake buk'ata nabama baiwa d'aya da kud'i takaima Sarkin Mota yabama wani ya sayomin. Badansu Abdurrahman sun tashiba Na tadasu duknai musu wanka, shirin sune yad'an jani lokaci abinka daba d'ayaba, gashi sunfara wayo, sauk'i nama d'aya Umimi babbar macece kuma Na yaba da tsaftarta. Duk da dai namusu gargad'in jira nazo Na had'a komai da kaina. A gurguje nayi wanka nasaka simple gown dabazata takurani wajen aikiba, nasaka k'aramin hijjab Na fito nabarsu Abdurraheem a d'akin, insha ALLAH bazasuyi kukaba, Dan saida cikinsu yay taf sannan Na fito. Naji dad'in iskesu sunci rabin aikin, to kusan su 15 kowa da abinda yakeyi. Dannan nasaka hannu nima wajenyin abinda yakamata ace ni nayi d'in, Dan Sarkin Mota yakawomin sak'ona tuni. Sannan ankawo sauran kayan daga sashen mama Fulani. 8:00am dai-dai Galadima ya shigo sashen, saboda yazo yay shirin massalaci, mamaki ya kamashi jin k'amshi ya baje ko'ina, shidai yasan bai tanadi komai d'aya danganci abincin salla ba. Yana cikin tunanin Sauban ya shigo d'auke da k'atuwar ledar kayanda zai saka, Wanda tun muna India yabada umarnin a dink'a masa su. Tare suka shiga sashensa da tunanin ko inacan, dukda yasan bazanbar y'an aiki akan girkiba, Dan yakula inada son komai naima kaina musamman girki. Babu abinda ke tashi sai k'amshi mai dad'i anan d'inma, ga ko ina yayi k'al gwanin sha'awa da birgewa, saidai kuma tsit alamun babu kowa. Sauban ya Shiga bedroom d'insa da kayan shima yana biye dashi. Cikin sigar tambaya Galadima yace, “to ina take itada yaran?”. K'aramar dariya Sauban yayi, yace, “Yaa Sam kasan halin auntyn tamu dai, Na tabbatar k'amshin girkinnan daga sirrin iyawartane, kaga kenan tana kitchen ”. Hararsa Galadima yayi, Sauban ya rufe baki Dan tuna ta6argazar da yayi. Ina cikin aikin Sauban ya shigo, bayin duk suka zube suna gaisheshi, da farko nama zata ko Galadima ne, saida Na waigo naga Sauban. Bayan ya d'aga musu hannu dabasu izinin tashi ya kalleni yana fad'in “Aunty gimbiya kinsani jin yunwa mai yawa da wannan k'amshin girkin naki”. Murmushi nayi kawai ina wanke hannayena, nace “ALLAH Yaa Sauban akwaika da tsokana, ya gajiya”. “Ai tabi gado wlhy, tare muka shigo da Yaa Sam fa”. Nace, “Ok". Coffee Na had'a masa a k'aramin filas Na d'ora a tire mai k'yau da mug daduk abinda zai iya buk'ata. Kar6a Yaa Sauban zaiyi nace, “A'a kabarsa Na hutar dake nikam”. Yay murmushi, “shikenan Aunty, inagafa nima zuwa zanyi Na shirya yau idin Na musamman ne ga jama'ar masarautar gagara badau”. “Gaskiyane Yaa Sauban, ALLAH yasa yau asamo mana amaryarmu”. Dariya yayi yana yunk'urin fita, “lallaima Aunty d'an k'araminnan dani wazai ban y'arsa?”. Ban samu bashi amsaba ya fice, Nima sashen Galadima Na Shiga INA murmushi. Babu kowa a falon, Dan haka Na wuce bedroom d'insa. Sallama nayi kawai Na shige. A bakin gado Na iskeshi zaune d'aure da towel, da alama wanka zai Shiga. Murmushi mukaima juna. nace, “Afuwan my King, aiki ya d'auke hankalina bansan ka shigoba”. Murmushi ya kumayi yana wani lumshe ido, Na ajiye tiren saman k'arim copy table d'in gabansa sannan Na zauna kusa dashi Na kwantar da kaina gefen kafad'arsa bayan Na sumbaci damtsen hannunsa”. Shima saiya karkato fuskarsa gareni ya shafa tawa fuskar da tattausan hannunsa, cikin magana rad'a-rad'a yace, “miya kaiki aiki keda ke tare da gajiya?”. Idanuna na d'ago na kallesa ina murmushi, nace, “my king ai yakamata ace anyi abincin salla a sashen Galadima, wannanfa shine karon farko da zakayi bikin salla da matarka a masarautar nan, bai kamata ace anyishi babu wasu alamuba ai OK?”. Yanda nai maganar da kashe ido d'aya saida tsigar jikinsa ta tashi, yad'an lumshe ido da sumbatar goshina, sannan ya rad'amin “ALLAH yay miki albarka” acikin kunne. A saman la66a na amsa da “Amin”. Ya tambayeni yara nace, “suna d'akina, maybe ma sunyi barci. Bamu tsaya 6ata lokaciba muka Shiga na taimaka masa da wanka, sannan muka fito nahau shiryashi, dukda lokaci yaja a nutse nake masa komai, danshi ma'abocin son komai a nutsene, bayason gaggawa ko yawan sauri koda a magana ne kuwa. Inamasa shiri yana shan coffee, kaga d'an gatan Munaya.😂 Tsaf na shiryashi cikin farar shadda daduk salla yakanyi amfani da ita wajen idi, nakawo babbar riga na saka masa sannan na fesheshi da turare, ajiye mug d'in hannunsa yayi yana d'aukar hularsa zanna bukar daketa maik'o yay mata kari ya kafa bisa kansa yana dai-dai tawa. Alk'yabbar dazai sa nagama feshewa da turare sannan na matsa ina kwantar masa da sajensa dayasha gyara da cumb, shikuma yana saka link d'in hannunsa. Kusan tare muka gama, na kama hannunsa na d'aura masa agogon dabai San da shiba. Da mamaki ya kalleni amma saina janye idona ina murmushi da fad'in “Happy salla nane nida triplets d'inka”. Rasama mi zaice yayi, sai kallon agogon da koshi da kansa iya mak'urar za6ensa kenan. Yakai hannu zai rik'oni nai baya kad'an ina girgiza masa kai, Dan nasan makomar rik'onin. Cikin marairaice face nace, “please kabari saika dawo kawai”. Wani miskilin murmushi yayi yana cije lips. Nima na murmusa da nuna masa Alk'yabbar. Kansa ya girgizamin a hankali yana mai shafa agogon Dana d'aura masa da d'ayan hannunsa. “kibarta zasumin nauyi da yawa, idan zamu fita gaida Governor zan saka”. Ido d'aya na kashe masa da had'e yatsuna👌🏻alamar yayi. Ya murmusa shima yanamin jinjina👍🏻. Ban barsa ya fitaba saida namasa photo biyu, sannan na rakoshi har falon k'arshe, inda Muftahu da Matawalle ke jiransa, suma sunsha wanka mai birgewa, tamkar ka sacesu ko anguna ranar aurensu. Galadima ya kareni da bayansa tareda min alamar na koma. Baya buk'atar su ganni kenan. Nima saina juya ciki kawai. Yayinda nake jiyosu suna masa Sheri da kod'a wankan nashi. Na lek'a yara naga barci sukeyi, Dan haka na koma kitchen muka cigaba da aikin da fatan mu kammala akan lokaci. Tunda matasan samarin masu d'anyen jini suka fito sai kallo ya koma sama, bayi sai zubewa suke suna gaishesu, sukam sai d'aga hannu dad'an murmushi. Haka kawai sai Galadima yaji kewar Harun, aduk irin wannan ranar shike zuwa ya fiddoshi daga sashensa, amma yau gashi bak'in halinsa yasa a gidan yari zaiyi tasa bikin sallar dagashi har ubansa. Ya k'aunacesa saboda ALLAH ashe shid'in ba haka bane a tashi zuciyar. Motocin da aka tanada domin su suka shiga. Wambai da talba haushi ya kamasu, ganin wai yau d'an uwansu matawalle ne zai tafi salla tareda Galadima. Oho, daga matawallen har Galadima basusan sunayiba. A 6angaren Abie da mai martaba shiga sukayi iri d'aya, Abie ya fito a ainahin sarakinsa na asali, sai rama wadda kayan jikinsa suka 6oye, idan ka gansu bazaka ta6a banbanta wanene sarkin ba. Mai martaba ya fito rik'eda hannun d'an uwansa Abie, nanfa aka fara ruwan cameras dukda dogarai na karewa ma, cikin lullu6esu da manyan riguna da musu kirari da busar algaita suka shiga mota d'aya. Masallaci yacika mak'il da al'ummar manzon ALLAH (s.a.w), isowar Sarki da tawagarsa kawai ake jira. A dai-dai k'ofar baya ta musamman motarda ke d'auke dasu Abie ta tsaya, mai martaba ya taimaka masa ya fita suka shige cikin massalaci. Nan take aka d'auki kabbara bisa umarnin liman domin nuna godiya da al'ajabin hikimar ubangiji na dawowar tsohon Sarki cikin k'oshin lafiya, bayan tsahon shekaru daya d'auka baya k'asar. Duk matashin dake k'asa da shekara talatinma bai sanshiba. Mak'iyan 6oyefa da sukaga tabbas sai tsoro ya kamasu, ashedai zancen daya karad'e gari gaskiyane, yau ga Sarki Saifudden Abubakar a gabansu ko sunaso ko basaso kuwa. An gabatar da Kud'uba tamkar yanda addini ya tanada, mai ratsa jiki da 6argo, mai k'arama muminin kwarai imani da tsoron ALLAH. Su Galadima suna jerin sahun farko, saidai na kusada su Abie ba. Alhmdullah, sallar idi ta gudana bisaga farincikin kasantuwar bayin ALLAH wannan rana da ko yaro k'arami ke d'okantuwa da zuwanta, bare su Galadima da jama'ar masarautar gagara badau da farin cikin ya had'e musu biyu. Bayan idar da salla akaja addu'a mai tsayin gaske ga Abie, sannan aka bashi microphone daga zaune yay bayani mai gamsarwa da ratsa jini da jijiyoyi Wanda yasaka mafi yawan jama'ar dake massalacin hawaye. Hatta da Galadima k'asa kawai yayi dakai yana murmushi da share hawayensa da handkerchief. Yau dai kam ai saida aka kai kusan 11:30 a massalaci kafin a sallami jama'a. Yayinda manya kuma suka samu yin gaisuwa ga Abie da masa murna da addu'a. A can kuwa jama'ar gari kowa ya gumtsi labari yatafi fesarwa, hakama y'an jarida masu zuwa kallon zahiri, kafin kace mi labari ya cigaba da shiga lungu da sak'o, hakama hotunan Abie da nasu Galadima. Bisa ga wannan labarine su Ahmad tahowa Masarauta dukda basuda tabbacin ganin Galadima d'in. K'arfe 12 aka shirya liyafar cin abincin a masautar, wadda har governor zai halarta, itace madadin hawa da akeyi zuwa gaida Governor. Duk yanda Galadima yaso komawa ga iyalansa hakan ta gagara, yawan jama'a ya hanashi matsawa konan da can, kowa soyake ya nuna masa kansa a jerin masu tayasa murnar dawowar mahaifinsa cikin k'oshin lafiya. ********** Alhmdllh munsami kammala komai, Na barma su Umimi sauran aikin suka k'arasa, niko nanufi tsaftace jikina kafin mijina ya shigo, dukkan abincin da za'a fita dashi kuwa nabama su Umimi umarnin kaisa duk sashen daya dace. Galadima daya tuna da batun abincin da Munaya keyi yad'an fita daga cikin mutane yana kiran sarkin Mota, Umarni yabashi akan zuwa birnin gayu ya kar6o drinks wajen manager, yanason kiran Munaya amma babu dama, Dan dawuyama idan ta maida layinta Na 9ja bisa waya, gashi bashida damar tsallakewa ya taho gareta. ********** Sosai Momma take samun tattali ga mama Fulani, ita abinma mamaki yabata, saida aka sakko idi sannan aka kaita sashe Na musamman da akayi aikin gyarawa da safiyar, zasu d'an zauna anan itada Abie kafin asan abinyi gameda sarautarsa dake kan d'an uwansa. A tsorace mama Fulani take, dukda kaffa-kaffa da take dasu Momma, ko kad'an batason mulkinan yabar hannun d'anta, har yanzu burinta jikokinta su gaji masarautar gagara badau. Amma dai taita danne zuciyarta Dan karta nuna hali. ****************** Bayan mai martaba da Abie sun huta aka fara gudanar da liyafar cin abincin a babban d'akin taro Na masarautar. Wanda yasamu halartar manyan mutane dake cikin binin, duk wani mai fad'a aji ya garzayo masarautar Dan kar ayi babushi, kokuma ya shiga black list. Matawalle ya kalli Galadima dayak'i cin komai sai drink yake sha. “Lafiya kuwa Sameer?”. Galadima ya kallesa da alamar tambaya, amma baice komaiba. Da hannu Matawalle ya nuna masa abincin gabansa. Murmushi Galadima yayi yana shafa kumatunsa, cikeda k'asaitarnan tasa yace, “Bazaka gane bane d'an uwa, my mata tayi abincin salla, idan naci wannan cikina ya cika naje can kuma babu space ai sai a hanani.......”. Sai yay shiru bai k'arasaba. Mi Matawalle da Muftahu zasuyi inba dariyaba, har mutanen dake d'an gefensu suka juyo suna kallonsu. Galadima kam murmushi kawai yayi ya maida eyeglasses d'insa a ido yana kallon inda su Abie ke zaune. Anci ansha kowa yay mak'il cike da godiyar Ubangiji, daganan aka fara gudanar da jawabai Na godiya ga ALLAH bisaga ni'imar dawowar Abie. Mai martaba shine ya fara, sannan Abba hayatudden. Maganarsu ta ratsa zukatan mutane da dama, domin sun nuna k'auna mai yawa da farincikin dawowar d'an uwansu, hakan ya k'ara musu kima, dan sunture zancen nan Na mutane a zuciyarsu, wato y'an ubanci dayafi komai ruruta wutar k'iyayya a masarautunmu Na Hausa Fulani. An buk'aci ganin Galadima shima. Ya mik'e cikeda takun izza da zagayawar jinin Mulki a dukkan sassan jikinsa, k'asaita da kwarjinin yarinta Na d'awainiya dashi. Yanda akaita zubama su mai martaba hototuna shima hakanne. Da yawan mutane dake wajen ya burgesu, koda haushinsa kakeji kwarjininsa ya Isa jin ka k'aunacesa lokaci d'aya. Ya gyara tsayuwarsa yana wani k'asaitaccen murmushi mai tsada da nuna halin dattako, cikakkiyar sallama ya musu suka amsa, sannan yacigaba da magana yana zare eyeglasses d'insa. Hawaye cike da idonsa yace, “A watannin da bazasu cika shekara ba Na tsaya a gabanku kamar haka ina kuka da kausasan kalamai ga dukkan mai hannu a ciwon mahaifina, a ranar d'aurin aurena hakan ta faru, nasan kuma dayawanku dake nan suna a wancan zaman, sai dai bisa ga hukuncin Ubangiji yau nine tsaye a gabanku ina kukan farinciki da tausasa harshena Na Neman afuwa, na godema Ubangiji da yaymin dukkan sutura ta rayuwa, ina fatan samun ta gaba inda yafi gidan duniya, badan nafi kowaba yaymin wad'anan ni'imomin, sai Dan hak'uri da juriya da kar6ar k'addara aduk yanda tazoma bawa, bara nabaku wani labari kad'an, Wanda yana d'aya daga cikin babbar riba dabazan manta da itaba har k'arshen numfashina. Doctor Arjun shine likita na farko daya fara duba Abie, shine kuma yacigaba da kulawa dashi har nakai wayo, shi mabiyin addinin Hindu ne, sanann daga wannan k'abila ya fito, shekarar dazan shiga jami'a sai ALLAH ya jarabcesa da ciwo rana tsaka, yanama cikin aiki a asibiti ya yanke jiki ya fad'i, y'an uwansa doctors sun bashi dukkan taimakon gaggawa harya farfad'o, a daren ranar saiya buk'aci d'aya daga cikin doctors d'in daya kira masa ni. Ina tare da Momma da Jakadiya kiran ya iso gareni, munyi mamaki kwarai da gaske, dan bamu dad'e da duboshiba, lokacin salla dayayine yasakamu baro d'akin dayake ma. Haka Na tashi natafi amsa kiransa. Awajen doctor Arjun Na iya yarensu na Hindu, tunda Na shigo saiya shiga muk'omin hannu alamar nazo garesa, nabi umarninsa Na zama kusa dashi tareda rik'e hannayensa cikin nawa, muryarsa cike da rauni yace___”. _“Sameer Kasan miyasa nace a kiraka kuwa?”._ “Kaina na girgiza masa alamar a'a. yayi murmushi idonsa Na cigaba da tsiyayar da hawaye, yakuma damk'e hannuna a cikin nasa yana cigaba da fad'in___”. _“Sameer kune Muslims na farko dana ta6a mu'amulla mai tsayo dasu, daga gareku na fahimci wasu k'yawawan halaye da kullum duniya kefad'in baku dasu, lallai duk mai ambatar wannan addini da addinin y'an ta'adda ya jahilci fahimta da sanin halayyar d'an adam, kun kasance masu hak'uri wajen samu da rashi, kar6ar rayuwa a dukkan halin data zo muku, kun kasance masu yawan k'yautata zato, mutane da yawa sunsha zuwa duba mahaifinka, amma duk d'unsu ban yarda dasuba amma Ku sainaga babu wani kokwanto a Kansu, da zuciya d'aya kuke k'ar6arsu da mu'amulantarsu, dukda zukatanku sunada yak'inin dolene a samu mugaye a cikinsu, a duk daren duniya idan nashiga duba mahaifinka nakan iske mamanka tana salla ko karatun littafinku, ahankali sai wad'annan abubuwan suka fara kwad'aitamin wani abu daban, tun ina kokawar turewa harya fara zama babban 6angaren tunanina dayay tasiri mai girma a dukkan kuzarina, da farko tsoro nakeji, Dan kaf ahalinmu babu wani mabiyin addinin musulunci ko kiristanci. Amma kasan duk miye matsayar wannan labarin danake baka a yau?”._ “kaina Na girgiza masa jikina a sanyaye, yayd'an murmushi da cigaba da fad'in__”. _“Inason biyan ko nawane domin Shiga addininku, a yau bana tsoron kowa yasani koya ganni a ciki, inason ribantuwa da k'yawawan halayenku”._ “A lokacin kunsan miya faru?”. Jama'a suka amsa da a'a. Galadima yay murmushe da share hawayensa da Handkerchief. “Na tsinci kaina cikin zumud'i da firgici dukda k'ananun shekaruna, Dan lokacin bazan wuce 17years ba nake tunani, hawaye Na zuba a idona nace da gaske zaka musulinta Doctor?. Cikim jinjina kai ya tabbatar min. Ban tsaya 6ata lokaciba nace doctor addinin musulunci ba'a biyan ko sisi domin kasantuwa a cikinsa, imani da ALLAH da yarda da manzonsa shine babban farashi mafi daraja a duniya. Yace to a ina zan samo imanin?. Nai dariya da fad'in ta hanyar ambaton Kalmar la'ilaha illallah muhammadurrasulullh. Yace to ya shirya. Duk da k'arancin shekarunan nawa baiyi Girman kaiba ya kar6a kalmar shahada yana mai jaddadata a harshensa har saida tari ya sark'esa, rikicewa nayi Na mik'e da nufin nemo doctor amma saiya hanani, yamin nuni dana bashi ruwa, haka nadawo na bashi ruwan, kur6arsa hud'u ya janye kansa yana fad'in___”. _“Sameer, tabbas yauce ranar tafiya koda shiri ko babu, ina rok'onka koda sau d'ayane ka gudanar da salla a kaina, sannan karka yarda wani d'an uwana ya san da musuluntata, badon komaiba sai Dan gudun tozarta ku, ka sanarma Anania ina matuk'ar k'aunarta, karta manta dani”_. Daga nan ya shiga maimaita kalmar shahada yana wata irin zufa maiban tsoro, na rik'ice inata ambatar sunansa da girgizashi, sai kawai naga jikinsa ya saki. Sakinsa nai Na fita da gudu kiran doctor sai mukaci karo da Momma dataji shirun yayi yawa tabiyo sawuna. Rik'eni tayi tana tambayar lafiya?, jikina Na rawa nasanar mata abinda yafaru da Hausa. Dan nasan mawuyacine asamu maijin yaren a kusa damu, hanani kiran doctor tayi taja hannuna muka k'oma d'akin tana share hawen farin ciki Dana kewar Dr Arjun, tai addu'a mai yawa akan gawarsa sannan tace Muh'd zaka iya masa wanka?. Bak'aramin tsorata nayiba, jikina Na k'yarma nace Momma wankafa?, nidai tsoro nakeji. Ta dafa kafad'ata cikin k'aramin kwarin gwiwa tace yarona karkaji tsoro, tunfarko ubangijine ya za6eka ya k'addara Dr Arjun ta hannunka zai zama musulmi, ka daure ka cika masa wasiyyar daya barmaka ta sallatar gawarsa, Dan kasandai su ahalinsa ba irin wannan jana'izar zasuyi garesa ba, ina tare dakai kaji. Bisa Umarnin Momma da koyarwarta naima gawar Dr Arjun wanka, itakuma tana bakin k'ofa tanamin gadi, Ubangiji kuma saiya ara mana dogon lokaci harna gama na maida masa Uniform d'in asibitin a jikinsa, sannan na sallacesa ina kuka. Saida muka gama komai sannan muka fito mukabar gawarsa cikin d'akin, bamukoyi nisa da k'ofarba mukaga doctor ya shiga d'akin da hanzari, mintuna kad'an da shigarsa maganar rasuwar Dr Arjun ta fara Shiga kunnuwan Mutane. Wannan rasuwa ta matuk'ar ta6a zuciyata, har a yau d'innan da nake gabanku ina jinta, kuma ban gaza wajen yimasa addu'oin samun rahama ba”. Galadima ya share hawayensa dake zirara tamkar fanfo, ya kalli mutane yana fad'in “kakannina, iyayena, yayyena da k'annenna kunsan hikimar baku wannan labarin kuwa?”. Jiki a sanyaye, wasuma hawaye sukeyi suka amsa da a'a. Galadima yay murmushi yana kuma share hawayensa da gyara tsayuwa, “Wannan labarin yana mana nuni muzama masu nagarta aduk inda muka tsinci kanmu, babu irin k'yawawan halaye da addininmu bai koyar damuba, amma son zuciya da burukan duniya saisu sauyamu, miyasa muke mantawa damu su waye? Ina kuma zamu koma?, dalilin ruk'o da gaskiya mahaifina ya fad'a hali mai tayar da hankali na tsawon shekaru, babu wanda ya ta6a tunanin sake ganinsa anan, amma kuma sai gashi, kunsan wane irin hali mai firgici da ciwo da muka tsinci kanmu kuwa? Mahaifiyata itace silar komawata jarumi, da taimakonta nazama jajirtacce, a halin k'uruciya har tunani nake anya kuwa tana sona? Ajiye sosayyar nan ta d'a da uwa tayi ta kutsani cikin talakawan daba yarena ba, ba addinina d'aya dasuba, ba k'asa d'aya muka fitoba, naringa wahalhalun koyon sana'oi da gwagwarmaya ta fahimtar rayu, ga karatu, ga damuwa da ciwon mahaifina, ban fahimci gata taminba saida na iya d'aukar nauyin ciwon mahaifina da hidimomin ahalina, na kammala karatuna bisa bigiren danake buri, iyaye mata wlhy kuzamto masu koyi da halayen mahaifiyata, matasa y'an uwana kuzama masu koyi da rayuwata, dukda ana ganina d'an ganta ban zauna gata yamin komaiba, saina tashi da k'afafuna da gumina na gina kaina, muzama masu k'yawawan halayya koda daraja martabar addininmu ga wad'anda basu fahimcesa ba, Dan k'yawawan hallaya da nagarta yaja hankalin Dr Arjun kwad'aituwa da addinin Islam, Yakuma mutu a cikinsa bisa amincewar ubangijin al'arshi, da mugayen hallaya mukeyi saidai doctor Arjun ya k'yamacemu dajin kuma k'yamar addininmu, son zuciyoyinmu shike maidamu bayan baya a Kullu yaumin, ba tarin dukiya ko gata ko k'yawune abin birgewaba, Nagarta, nagartar samun k'yawawan halaye da d'abi'u shi ake kira jarumta, matata ta ta6a fad'amin Hak'uri shi ake kira NASARA, saida hak'uri ake zama jarumi, sai an jure zafi ake tsintar kai a sanyi. Kusan shekarunta nawa kuwa?, ashirin, inhar mace mai k'ananun shekaru irin wannan tanada hikimar zance da nazari mai amfanar da wani irin haka miyasa tunaninmu ke d'aukar mace mai k'aramar kwakwalwane?, nabaku satar amsa kaje ka mu'amullanci matarka ta nagartacciyar hanya kaga yanda zaka amfanu da tagomashin tunaninta, kunga mata biyunan sun zamema rayuwata wata ginanniyar Katanga, mahaifiyata da kuma matata da auren shekara d'aya kacal zamu cika, kakata yayata k'anwar mahaifiyata rumface su dake kare martabata da zamana cikakken mutum, ina mai farin ciki mai tsanani da samun lafiyar mahaifina, da godiya mai yawa ga wasu ke6antattun mutane wadda gudunmawar suce silar ganina a gabanku, ALLAH ya albarkaci rayuwar ahalinsu ya cika musu burukansu na alkairi, Yakuma had'amu a aljanna gaba d'aya”. Duk suka amsa da amin suna binsa da tafi. Daganan sauran jama'a sukaita bayani d'ai-d'ai, taro dai bai tashiba sai kusan 3:00pm. Cikin farin ciki Galadima ya shigomin, ko kunyar su Ahmad dake zaune da Sarkin mota ya shigo dasu bai jiba ya rungumeni, saida na ankarar dashi sanann ya sakeni yana susar gefen wuya alamar yaji kunya, yayi farin ciki da ganinsu kuwa, yaran sun shiga ransa sosai, duk da abinda yayma mahaifansu basu tsanesa ba, saima zuminci mai k'arfi daya k'ullu a tsakaninsu. Ranar sashenmu saiya koma na matasan samarin masarautar, Dan shima Sauban nan ya kawo gayyarsa cin abinci, gasu Yassar kuma, itama Samha saiga tata gayyar, saikuma ga matasan gidanmu da y'ammata da banyi zaton ganiba, harda Zarah da Siyama, dad'i tamkar xai karni kuwa. duk yanda Galadima yaso ke6ewa da matarsa abin ya gagara, dansu Matawalle da Nuren da suka iso dawasu samarin masarautar suma duknan suka nufo, tsakaninsa da Munaya sai dai y'ar satar kallo, dan kwalliyarta tagama narkashi. Baniba kosu Amaturrahman sunji a jikinsa raranar, d'auka dai sun shata harsun gode ALLAH, bankuma samu damar shayar dasuba sai madara suka sha. Har dare babu wata damar samun ke6ancewa da juna. Washe gari kuma aka gudanar da hawan salla mai k'ayatarwa, wanda a tarihin masarautar gagara badau an dad'e ba ayi irinsa ba, saboda manyan sarakuna na garuruwa daban-dabanne da Governors harda uban gayya president da senators da sukazoma Abie barka da dawowa suka halarci bikin hawan sallar. Misalta muku k'yawun kwalliyar jarumin naku Galadima ai 6ata lokacine, ammafa komai zamm, y'ammata da yawa sun k'yasa, balle yau fuskarsa washe take da murmushi na musamman Wanda jama'a basu ta6a ganiba. Su Abbana ma sunzo gaida Abie, sun sami k'yak'yk'yawar karramawa mai ban mamaki, wadda tasani farin ciki mai tsanani dajin k'arin k'aunar Ahalin Galadima. ****** Saida shagalin bikin salla ya lafa nasamu zuwa gidanmu da zagaya dangi, kowa yayi farin cikin ganina, musamman ma Munubiya da Innarmu, su Aiyaan da sauran jama'ar gidanmu, jikin Innaro yayi tsanani, dan harma ana shirin kaita asibiti, ciwon k'afa ya takura mata ainun. Sati biyu dagama bikin salla tawagar masarautar su Momma sukazo daga Niger, a masarautar gagara badau suka sauka, kasancewar harda uban gayya Sarki. Wani k'warya-k'waryar biki zuwan nasu yazama a masarautar, tareda k'ulla alak'a mai matuk'ar k'arfi wadda ada babu ita, da safe Matan suka koma gidanmu akabar Sarki da jiga-jigansa anan. A wannan zuwane aka nemi auren Ayusher, saima Abbansu ya tak'aita musu wahala akan a d'aura auren kawai baki d'aya kowa ya huta. Kowa yayi murna da hakan k'wai da gaske..............✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼 [8/21, 8:44 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ______________________ *_My Ayusher Muh'd kema ga naki, a koda yaushe kina cikin zuciyar bilyn Abdull, alkairin ALLAH yakai gareki har gadon barci tawan_*😘😘😁👍🏻 *_Maman kadee kina ina, maza garzayo ki kar6i k'undumemiyar gaisuwa ga bilyn Abdull, ina yinki ever y'ar uwa rabin jiki, ked'in tadabance wlhy a gareni, ALLAH ya raya mana kadeen mu har lokacin aure mu kwaso shoki😂😘😘👍🏻🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀._* _____________________ *_BOOK 3_* 👉🏻3⃣1⃣ .................Randa sukaje gidanmu ai munsha kallo da mamaki, yau ga babban Sarki har cikin gida, dan Sarki cewa yay saiya taka har d'akunan y'an uwansa, hakan yayma Innarmu dad'i, koba komai jama'ar gidanmu zasu kuma ganin martabarta. Aiko sun gani, dan ko rantsuwa nayi babu kaffara wasu saisunyi kukan fili bama na zuciya kawaiba. Ranar anguwarmu cika tayi mak'il da jama'a. A wannan zuwane Innarmu ta fara taka nawa d'akin itama, dan tana zuwa gaida ahalinta masarauta saboda anan aka saukesu, dan haka Galadima yake sakawa a d'akkota duk bayan kwana 2 susha hirar zuminci, duk da Sarkine dawasu manyan y'an rakiyarsa ne kawai a masarautar, sauran mata dasu Badeerah duk suna gidanmu, wasu kuma gidansu Ayusher. Kwanansu goma ciff aka d'aura auren Yarima Issifu da amaryarsa Ayusher, wannan aure yasaka kowa farin ciki da annashuwa, anyi biki na kwanaki biyu anan muka shilla Niger kaita, a can kuma aka d'auro auren Badeerah da Yaa Fadeel, kwanakinmu Biyar anashan shagali maiban mamaki da birgewa, muka d'akko amaryar Yaa Fadeel muka dawo gida. Koda muka dawo babu zama, dan kuwa hidimar bikin aunty salama muka shiga, Wanda yanemi had'ewa Dana Muftahu da Matawalle, zakusha mamaki idan nace Muku Samha Ce matar Muftahu😁, wannan had'i ALLAH yayishine bisa umarnin Momma, kowa kuma ya kar6a da hannu biyu yay addu'a, koda Samha taso bijirewa bisa ga soyayyar Gopal nice naita tausarta da mata nasiha harta kwantar da hankalinta. Munsha shagali kam iya shagali, babu abinda zamucema ALLAH sai godiya dakuma bin amare da angwaye da addu'a. Aiko wad'annan bukukuwa sai suka tada tsumin Nuren shima, yace aure shima yakeso, kai tsaye kuma ya kawo Farhat d'iyar Minister a matsayin za6insa, su Papi basuk'iba, domin nagartar mahaifiyar yarinyar ya cancanci a aureta, hakan kuwa akayi, shima aka sanya bikinsa kusa, mukasha biki kuwa cikeda nishad'i da farin ciki. ************* Bayan kammala wad'annan bukukuwa mukajema Aunty Salamah gaisuwa, da tayata murna ta musamman ni da Munubiya, tarba tamana mai k'yau da mutuntawa, a hirar da muka gudanar nake mata tambaya gameda mitasani ga Galadima?, dan naga yaranta sun kasance yaransa na wajen aiki. Murmushi tayi tana sakama Meenal pampas, “Babu wata alak'a tsakaninmu, Ameer k'aninane uwa d'aya uba d'aya, sanan mu y'ay'ane ga Baba Rabilu da zakiji yana fad'a, har akayi aurenki da Galadima bansan akwai alak'a tsakanin Mahaifina da shiba, duk da nasan kad'an daga cikin labarin mahaifina, sai a dalilin satar Muftahu da mukayi, ta wannan hanyarne kuma mahaifina baba Rabilu yasamu ganawa da Galadima ma, akuma wannan lokacinne duk muka San komai gameda abinda yafaru, ashema yanakan Sani ya saka Ameer aikin C.I.D, bisa tsatstsauran bincike daya dad'a yanayine ya gano Galadima yanama hukumar DSS aiki, shiyyasa yatura Ameer ga hukumar dan neman kusanci dashi, wannan shine kawai abinda na sani”. Daga ni har Munubiya munsha mamaki da girmama hukumar Ubangiji, dan shine ya sanya alak'a tsakaninmu da aunty salamah batareda sanin junaba ko wani dalili, ni dai ALLAH yariga ya k'addara nice dama matar Galadima, shiyyasa ya kulla bisaga hikimarsa wadda wasu wawaye suka kalla a matsayin nasararsu. Satinmu biyu da zuwa gidan aunty salamah mukaje India ni da Galadima, halattar bikin Akash da Doctor Erfan Fahad, abin mamaki da al'ajab saiga Radha a matsayin matar Akash, matan Dana ta6a had'uwa dasu a shagon kayan yara na Galadima, lokacim inada cikinsu Abdurrahman, masu yara Vishnu, Ashe ita k'anwar Maman Vishnu d'ince. Aiko muka rungume juna cikin tsantsar farin ciki da annashuwa, ashema munsan juna, vishnu ya k'ara girma abinsa, sai dai bai ganeniba ma😊. Ana gama bikin Akash muka nufi Kashmir bikin Dr Erfan Fahad da tashi amaryar shima, nanma mun rakwashe mun kwalla kamar babu gobe. Daga nan muka dawo India muka baje kolin soyayya, duk da ni yanzuma banajin dad'in gidan babu su Momma, sainaita k'iyasta rayuwar damukayi aciki a baya, wani nayi kuka wani dariya, Ashe 6angaren Galadima ma hakance yafaru, rayuwa kenan tsarin ubangiji. Mune har k'auyen su Khumar, shima kuku munje nasu gida. Saida muka kwashe kusan watanni biyu a wannan zuwa sannan muka dawo bisa samun labarin rikicewar jikin innaro. A lokacin su Amaturrahman suna rarrafensu ko ina, harma sukan gwada mik'ewa tsaye, dan suna wata na 10 ne, danma tafiyar kamar tamusu nauyine. Isowar dare mukayi, dan haka washe gari tunda safe muka nufi asibitin da aka kwantar na innaro. Hankalina yatashi ganin yanda Innaro ta koma, dukta tsotse takuma tsufa. Na zauna bakin gadon ina kama hannunta da share hawaye, dukkan ahalin gidanmu mazata da mata na ma'auri suna asibitin. Innaro ta kalleni tana murmushi k'arfin hali, da ido taima Innarmu magana akan tazo kusa da ita. Innarmu ta share hawayen idonta ta k'araso gaban gadon ta durk'usa, hannuna innaro ta saki ta kama na Innarmu. Ahankali ta fara fad'in, “Ai'sha ki gafarceni, nasan na aikata miki kurakurai da zalunci iri-iri, na manta da duniya bakomai bace a wajen Bawa balle kayan cikinta, idan babu mutuwa akwai tsufa, babu abinda ke dawwama sai ALLAH, duk yanda ka d'auki kanka hakan kake kasancewa, ko a auren yaranan da y'ay'an alhaji halluru na zalunceki, amma nayi nadama tun a auren su da mazajensu na yanzu, y'an biyu dan ALLAH Ku yafemin kuma, amatsayinku na jikokina ban muku adalciba, son zuciyane kawai da rashin hangen nesa, yafiyarku itace babban gatana, ina kuma rok'onku kumin Afuwa domin ALLAH”. Atare ni da Munubiya da Innarmu muka had'a baki wajen fad'in, duk mun yafe miki Innaro, ALLAH ya yafe mana baki d'aya, kin Isa damune ai, kuma Bawa baya zartama k'addararsa da bitar rubutaccen littafinsa tundaga cikin uwa. ALLAH ya baki lafiya dai. Innaro tayi murmushi mai ciwo tana hawaye, ta juya ga y'ay'anta su Abbanmu da gwaggo Safiyya suma tana Neman gafararsu. Suma duk d'urk'ushewa sukai a k'asa suna Neman tata gafarar, matan gidanmu duksai jikinsu yay sanyi, suma suka durk'usa suna Neman gafararta, ta rok'esu akan suma su canja Dan ALLAH. Cikin awannin dabasu gaza biyuba mai afkuwa ta afku, dan kuwa ALLAHn daya bamu Innaro yau ya d'auke abarsa, ta koma garesa tafiya mai nisan zango, saiga su baba k'arami na kuka da idanunsu, mahaifiya dabance, komai mugun halin mutum idan giji tazo dolene ka saduda dajin k'aunarsa ta musamman, kuka kam mun cisa tamkar babu gobe, yau gidanmu saiyay tsitt. Gwaggo Safiyya ta mata wanka a d'akinta, aka sallaceta a k'ofar gida da raka gawarta gidanta na gaskiya, hardasu Galadima kuwa, Wanda shima saida ya share hawaye, halayyar tsohuwar kan sakashi nishad'i haka kawai, danshi bayajin haushin masifarta, saima birgeshi da takeyi, musamman idan ta kafe akan Abu, bayan tasan gaskiyane amma tace sam ita ba hakaba. Ranar a gida muka kwana harsu Fauziyya, washe gari aka cigaba da kar6ar gaisuwa, a kwana na biyu saiga dangin su Innarmu daga Niger, harda Ayusher dake fama da tsohon ciki. Ranar addu'ar uku saiga su Abie da mai martaba sunzo gaisuwa suma, dasu akayi addu'ar uku ma. Aranar duk muka koma gidajenmu cikeda kewar innaro. ********* Ranar addu'ar bakwai d'in Innaro muka samu shiga wajen baba mai kanwa ni da Galadima. Mun iskeshi shima dai lafiyar sai a hankali, dan yanzu ko fitama bayayi, muka gaidashi cikeda girmamawa, ya amsa mana da fara'a, harda tsokanarmu da cewar, “Sai yau nake ganin ango da amarya?”. Duk murmushi mukayi cikin jin kunya. Shima ya kuma murmusawa da fad'in, “Mi kukeson Sani y'ay'ana?”. Nace, “Baba mai kanwa abinda ALLAH ya baka ikon Sani game damu”. d'an Murmusawa yakumayi yana gyara zaman hularsa, ya nisa cikin sauke numfashi. Yace, “Da farko dai niba maye bane, bakuma muguba kamar yanda wasu sukasha fad'a tun ina yaro, saidai ina tare da wasu aljanu da bansan ta Yaya suka kasance daniba tun k'uruciya. Tun farkon zuwan kakanninki gidan Malam fharuku aljanun dake tare dani suka sanarmin da dukkan asalinsu, harkuma suka rasu da matsalolin da mahaifiyarku taita fuskanta ga marigayiyya, abinda yasa na barsu ban ta6a maganarba saboda komawarsu a wancan lokacin bashida amfani, ina tausayinsu kuma k'warai da gaske, aljanuna sunsha d'aukata su kaini har cikin masarautar su Ai'sha, kullum cikin bibiyar musu ko ansamu canji nake, amma ba'a daceba har ta samu haihuwarku. Abinda yasa lamarin Galadima ya shigo rayuwaki a labarin shine, Maharbi daya taimaki Badi a jeji ranarda ya bama Auwalu babanki abin d'aukar hoto ne. Ba mutum bane wancan maharbi, aljanine yazo masa a suffar mutane, kuma har Badi yabar wajensa shima bai saniba, wannan aljani shine ya ta6a taimakonka a India lokacinda ciwonka ya tashi ka fad'i a titi, shine kuma ya kwad'aita maka wasu zantuka akan matar dazaka aura, a lokacin shekarun su Hussaina 12 kacal a duniya😊, badan yasan itace matar takaba ya fad'a, saidan maka fatan hakan, dan yata6a sanarmin akwai al'amari mai k'arfi dake tattare da y'an biyun Ai'sha, kuma bisa dalilin abinda akabama Auwal abin yake, sai dai shima baisan mineneba, saidai mujura hukuncin ALLAH. tun daga wannan lokacin wannan aljani ya baza y'an uwansa aljanu suna kula da dukkan motsinka Muhammad Sameer, suma su Hussaina haka itada y'ar uwarta har suka kai adadin shekarun girma. Yafara zuwama Hassana a mafarki, amma saiya fahimci batada k'arfin zuciyar da zata iya shan gwagwarmayar rayuwa dakai, hakanne ya sakashi komawa kan Hussaina, amma ita sai aka dace, wannan shine mafarkin da kuka dingayi keda y'ar uwarki Hussaina, nikuma na cigaba da d'oraki mataki-mataki akan kar6ar Muhammad a matsayin miji, Haidar da kike gani yazo har aka saka ranar aurenku ba mutum baneba, aljanine dagashi har iyayensa da sukazo neman aurenki”. Ba k'aramar zabura nayiba, hartaso bama Galadima da baba mai kanwa dariya. “Kinga kwantar da hankalinki, ai ko driver dayay masu Muhammad aiki akan satoki ba mutum bane ba, k'arfin jini da ALLAH yabaki kikaso fahimtar hakan kuma, daga ke har Muhammad kunsha mu'amulla da aljanu a matsayin mutane ai har lokacin da ALLAH ya k'ulla igiyar aurenku, aiko cikar taron d'aurin aurenku akwai d'unbin aljannu da suka Halarta a ciki, dukkan bayanan danai muku yanzu zan baku tabbaci, wani turaren tsinke ya d'aga lamusashshiyar katifarsa ya zaro, ya k'yarsa ashana ya kunna, dandanan hayak'i da k'amshi ya gaurasye d'akin, saiga sallama munji a k'ofar d'aki. Matashin saurayi ya shigo, Wanda Munaya bazata ta6a mance fuskarsaba, wato Haidar, hakane ya sakata zabura ta mak'alk'ale Galadima. Haidar yay murmushi kawai yasamu waje ya zauna, saiga kuma dattijo da Galadima yata6a had'uwa dashi a India, shima dai da kallon k'urilla ya bishi, basu fita a mamakiba saiga Driver daya ta6a d'akko Munaya lokacin dayace suyi auren Contract shima ya shigo, saikuma mabanbanta fuskoki Wanda sun had'u dasu a mabanbanta gurare, harda masu zuwama Munaya a k'awaye, saida duk suka zauna suka nutsu sannan suka gaisa da baba mai kanwa, Galadima ma dai a d'arare ya yarda yabasu hannu sukayi musabaha, nikam uwar y'an tsoro ai ina mak'ure a bayansa, ALLAH ma yasoni banzo dasu Abdurraheem ba, suna gidanmu. Baba mai kanwa ya nuna manasu yana fad'in, “Ina fata duk kun ganesu?”. Duk muka amsa da eh a d'arare. Dattijon daya had'u da Galadima a India ne yafara magana a nutse, “Muhammad Sameer ya bayan rabuwa da gwagwarmayar rayuwa?”. Galadima ya amsa da “Alhmdllh”. Tsoho mai sihirtaccen k'yawu zam jinin indiawa yace, “ka tuna na fad'a maka matarka Ce fitilarka? zuwa yanzu ka tabbatar?”. Galadima ya gyara zama yana Murmushi har hak'waransa na bayyana, yace, “Lallai ban mantaba kaka, saidaima nabama wasu labarin, nakuma mik'a godiya ta musamman agareku da fatan ALLAH ya had'amu daku a aljanna, ya kuma biyaku da mafificin alkairi bisaga taimako na mussaman da kuka bama rauwarmu ni da matata, duk da kasancewarmu ba jinsi d'ayaba”. Gaba d'aya suka amsa da amin, haidar ya nema izinin Galadima domin Neman afuwar Munaya. Galadima ya bashi izini. Haidar yace, “ki gafarceni bisa ga kalmomi masu zafi dana fad'a a gareki a wancan lokacin, hakan ta farune bisa k'ok'arin janyo hankalin mijinki domin jin tausayinki, kasancewarsa mutum mai tausayi da gudun shigar wani matsala ta dalilinsa”. Munaya ta murmusa tana kallonsu. Tace, “na yafe maka wlhy, kuma komai yawuce, fatana ALLAH ya tabbatar da addu'ar mijina a garemu baki d'aya”. A tare aka amsa da amin. Mun dad'e muna tattauna abubuwa da dama, kafin daga bisani sumana sallama su tafi, Wanda bai saniba saiya d'auka da gaske mutanene, baba mai kanwa yay mana doguwar nasiha mai ratsa jiki, wadda harta d'arsa tsoro a ranmu, yakuma ja mana doguwar addu'ar. Galadima ya ajiye masa alkairi mai tsoka mukayi masa sallama muka fito, bamu dad'e a gidanmuba muka koma gida jikinmu a sanyaye da abubuwan da suka faru tsakaninmu da baba mai kanwa da su Haidar. Kwanaki uku da faruwar haka labarin rasuwar baba mai kanwa ta riskemu, mutuwarnan itama ta girgizamu k'warai da gaske, munkuma jema iyalansa gaisu. Manyan dake kula da matsalolin gidanmu duk Ubangiji ya d'aukesu, yau babu Innaro babu baba mai kanwa. Zuwa yanzu kam ko ina su Amaturrahman zuwa sukeyi, sunyi wayo sosai da girma, hakama yaran Munubiya danasu Safara'u datai hak'uri takoma gidan mijinta suke zaune lafiya da kishiyarta da haihuwa yau ko gobe. Ayusher ta haihu namiji, dan haka muka d'unguma Niger suna k'wanmu da kwarkwata, hardama y'an gidanmu Wanda wanannne zuwansu na farko, sunkuma gano abinda yafi k'arfin shirmensu kuwa, yayinda girman Innarmu yakuma yawaita a zukatansu. Mun dawo da kwana hud'u Aunty Salamah da Badeerah matar Yaa Fadeel suka sauke, babu nisa tsakaninsu Farhat d'in Nurenma ta juye, Saiga Samha ma ta haife yaranta y'an biyu duk mata, hakama matar Matawalle. Kai wannan abun dad'i da yawa yake, munsha shagulgula sunan kam babu k'arya. A lokacin ne kuma Galadima yafara k'orafin na yayaye su Abdurrahman wai kona samu nima. Dan gatan da ALLAH yay mana ni da Munubiya muna jerin mata da al'ada ke d'auke musu bayan jinin bik'i har sai sun yaye, amma nasan murzar da Galadima ke min da tuni k'ila ciki na uku na d'auka🤭🤣. Yanzuma danake kwance a jikinsa dariya kawai nayi. Nace, “su Abdurraheem basu gama yin k'wariba my king, inama laifin sud'anyi 4years haka?”. Harara ya zubamin da fad'in, “yarinya kinma isa, insha ALLAH gab kike da d'aukar wasu ukun”. Bance komaiba sai dariya da nayi ina sumbatar goshinsa domin kauda zancen, dan inhar yay zurfi zai zama rigimar da muka sabane kawai, nikuma bana buk'atar hakan. ★★★★★★★★★ Rayuwa ta cigaba da gungurawa dai-dai gwargwadon iko, yau da dad'i gobe babu, soyayya nida mijina ba'a magana. Shekarun Abie biyu kenan da dawowa cikin ahalinsa, yayinda kunnen kowa na masarautar gagara badau yake a bud'e dan sonjin makomar sarautarsa. Saidai kuma tsit babu wani bayani. Yay shiri yaje har prison wajensu Harun jikin su Alhaji Mansur yayi sanyi matuk'a, Wanda sukaso ya k'are rayuwarsa tamkar gawane a gabansu, lallai duk saurin Bawa da son nuna k'arfin iko sai ya jira ALLAH, Abie baice dasu komaiba ya juyo ya fito, shiruma maganace ga mai hankali. A 6angaren mai martaba sunata fafatawa ne shida mama Fulani tun dawowar Abie, yanason tado da maganar sarauta amma mama Fulani ta kasa ta tsare, ta hanashi. Yayinda gimbiya zulfah keta k'ulunboton asirce-asirce agefe dan kar mulki ya koma wajen Abie, duk da batada wata fawa a masarautar yanzu, saboda tunda wancan abun ya faru mai martaba ya hanata shiga turakarsa, babu kuma wani Abu dayake mata a matsayin matarsa, bai kumace ya saketa ba, dan kowa yasan Sarki a k'asar Hausa baya saki, saidai idan mutuwa ta raba. Da farko tashiga damuwa tamkar tayi nadama, amma dawowar Abie saita kuma birkicewa, musamman da Matawalle yay aure matarsa kuma ta haifi mace, duk zugarta dason 6ata Galadima a wajen y'ay'anta Matawalle baya d'auka, saima yakuma kusantar Galadima suka d'inke waje d'aya, su wambai ne dai ma sai kuma rura k'iyayyarsa suke a ransu, har Momma da Abie haushi sukeji, duk da jansu a jiki da sukeyi a banza, uwarsu da mama Fulani sun rigada sun hure kunnuwansu. Ganin abin zai kwa6e mai martaba ya shirya taro na manyan masarautar, harda gayyar papi Wanda ayanzu shima lafiya take Neman yimasa k'aranci, saboda girma, dan yanama shirye-shiryen yin murabus ya d'ora mahaifinsu Nuren. Mama Fulani batasan da wannan taronba ko kad'an, dan mai martaba bai nuna mataba ko da a fuska. Galadima na kwance a tsakkiyar falonsa yana wasa da yaransa daketa hawa jikinsa yana musu doki, ni dai ina gefe zaune ina danne-danne a laptop. Nakan kallesu nai dariya idan sukai masa wani Abu. Wayarsa dake kusa dani tayi ring, d'auka nayi na mik'a masa, ya sauke Amaturrahman dake saman fuskarshi yana duba wayar, ganin mai martaba sai ya mik'e zaune sosai yana musu alamar suyi shiru. Duk da ba wayone dasuba yariga ya koya musu hakan, duk kuwa sai suka rik'e bakinsu. Ni dai dariya nayi kawai na kauda kaina. Galadima ya amsa kiran cike da girmamawa. Yana yanke wayar ya mik'e. Kallonsa nayi da mamaki, “My king lafiya kuwa?”. “Duk'owa yay ya sumbaci goshina sannan ya zauna a hannun kujerar da nake zaune. yace, “Mai martaba ne ke buk'atar ganina wai yanzunnan”. “Tofa ALLAH dai yasa lafiya?”. “To amin, bara na kimtsa naje naji”. Na amsa masa da to. Yaran duk suka mik'e zasu bishi na kamosu ina lalla6arsu. “Haba my sweetness kuzo kuji, Abbu wanka zaiyi kunji”. Abdurraheem ya kwa6e fusaka zaiyi kuka, danshi duk yafi sauran y'an uwan k'ulafucin uban, ko barci yake Galadima yay magana saiya farka, gashi bashida yawan kwaramniya, yanda Amaturrahman da Abdurrahman zasu saki jiki suyi wasa Abdurraheem bayayi, idan har Galadima na gida to yana manne dashi. Koda ya fito zai tafi sai suka sanya kuka, lalla6asu yayi yay musu wayo ya gudu, amma Abdurraheem saiya saka kuka harda shashsheka yana shid'ewa, dole Galadima ya dawo da baya ya d'aukesa suka fita. Nikuma naita lallashin su Amaturrahman har suka saki jikinsu kuma. Abdurraheem yana ganin Abie sai kuma ya mak'ale masa, ya d'aukesa ya d'ora a cinya yana murmushi. 'Dakin taron yayi tsit kowa yana sauraren Mai martaba. Cikin nutsuwa da halin dattako yafara jawabi kamar haka. “Inama kowa fatan alkairi, nasan kowa zaiyi mamakin wannan taro na gaggawa, wasu dalilaine suka saka yinsa tilas, tun bayan kama mutane da suka cutarmin da d'an uwa babu wani zama da mukayi ko magana akan wannan matsalar, duk da kasancewar akwai namu mutane a ciki, waziri da d'ansa, da kuma sirikina, sai mahaifin mahaifiyata wato kakana kenan, tabbas abune da musalta bak'in cikin da mukayi 6ata lokacine, amma mun tura komai ga Ubangiji ya musu hukunci dai-dai da yanda suka aikata mana, a kullum kuma cikin yaba k'ok'arin d'anmu mukeyi bisa ga jajircewa akan tonuwar asirinsu, ALLAH ya albarkaci rayuwarsa da ta zuri'arsa, akwai wad'anda suka bashi taimako sosai, amma bamuyi musu komaiba. Bawai mun manta dasu baneba, sunan cikin zukatanmu. To a yanzu dai mak'asudin zamanmu anan shine inason maida sarautar dake kaina ga d'an uwana, tunda ALLAH yabashi lafiya, sai a d'ora daga inda aka tsaya”. Cikeda mamaki Abie ya kalli mai martaba, cikin Dakatar dashi ya d'aga masa hannu yana 6ata fuska. Sannan ya yunk'ura ya mik'e yana mik'ama Galadima Abdurraheem dayay barci, har yanzu bawai ya dawo normal bane, da taimakon sanda yake tafiya. Yace, “Ku gafarceni bisa katse hanzarin d'an uwana danayi, maganar gaskiya bazan kuma wani mulkiba, akwai iyayenmu anan yakamata su dubi lamarin bisa ga idon basira, har zuwa yanzu bawai lafiya Ce ta gama isataba, saidai muce Alhmdllh domin Ubangiji yamana dukkan Ni'ima, ai ko lafiyata k'alau zan iya sauka a wannan shekarun nawa na bashi dama, munyi maganarnan ni da shi nace yabarta anan, amma saida ya kawota, to wlhy, wlhy kunji dai na rantse ko, bazan sake hawa karagar mulkiba, kwanan nanma nake shirin komawa India ni da iyalina, dan ALLAH wannan maganar ta tsaya iya haka, karmu sake jayayya a kanta”. Shiru kowa ya kasa motsi, domin wannan rikici yazama na manya, hakanne ya saka papi mik'ewa ya sallami kowa, ya rage daga shi sai mai martaba da Abie a d'akin taron. *********** Na fito wanka na iske Galadima zaune a bakin gado hannunsa dafe da kai, da sasaarfa na k'araso dan nasan akwai matsala kenan, musamman da acikin y'an watannin nan sau biyu ciwonsa na tashi, duk da akowane bayan watanni uku sai munje India ganin likita shida Abdurraheem, dayake yanzu hankalinsa yana nan Nigeria akan Company da suketa k'ok'arin ginawa, zuwa India saiya zame masa sai time to time kokuma wani gagarumin Abu ya taso daya zama tilas saiyaje. Laimar ruwa da yaji a jikinsa ya sashi d'agowa da hanzari ya kalleni, kafin nace wani Abu sai kawai ya rungumeni tsam a jikinsa, sai kace zai maidani cikine, kusan mintuna 3 muna a haka, sai sauke tagwayen ajiyar zuciya yakeyi, nikam ina shafa gadon bayansa a hankali. Nutsuwar daya samu ta sakashi d'ago muka zubama juna ido, murmushi mai kashe zuciya namasa ina shafa sajensa, cikin sanyin murya nace, “Waye ya ta6amin Barden gagara badau ne?”. Lips d'insa ya ciza yana rik'e hannuna, cikeda damuwa yace, “Munaya sosuke kawai sudawo da abinda ya wuce”. Nace, “Mikenan?”. Ya sauke nannauyan numfashi ya zamewa ya kwanta, kansa bisa cinyata muna kallon juna yacigaba da fad'in, “Akan mulki mana, tun sanda Abie ya dawo na fuskanci Abba nason maida masa mulki, amma mama Fulani na hanashi, sannan a gefe mahaifiyar su Matawalle tana nata k'ulle-k'ulle, dama kwanaki mun fara maganar ni da Momma da Abie, saboda rikicin dake Neman 6arkewa tsakanin mama Fulani da mai martaba, a lokacin bansan kuma miya dakushe lamarinba, sai yau da rana tsakarnan mai martaba yace zai maidama Abie sarauta, wannan shine mak'asudun zaman gaggawar, kinsan kuwa wannan kujerar itace ke hana kowacce masarautar zaman lafiya da hargitse-hargitse, harta kai ga asarar rayuka, shiyyasa da Sarki yafara ciwo burin kowa ya mutu hattada y'ay'ansa da matarsa mai manyan y'ay'a saboda burin y'ay'anta su gaji mulki? Wlhy ina cikin tashin hankali, hankalinmu ya kwanta kowa yasamu nutsuwa a masarautar nan gawani bala'innan zasu 6alloma mutane, inaga kawai zamu tattara mu koma India harsu Abie da zaran anyi bikin Sauban. Da aunty mimi”. “Ina bayanka wlhy my king, wannan itace babbar mafita kawai, domin cigaba da samun zaman lafiya mai d'orewa, hukuncin daka yanke yayi sosai”. Ya lumshe idanu da shafo fuskata saboda jin dad'in goyon bayan dana bashi, domin k'ara masa nutsuwa saina d'ora bakina akan nashi nashiga masa wani salo mai cikeda kwarewa fiyeda yanda ya koya min, tamkar jira yake ya birkicemin, kafin kicemi labari ya canja salo, saigani da sake sabon wanka babu shiri.🤭 Tun daga ranar bamu sake jin maganarba daga bakin manya, sai munafunce-munafunce da sukaita wanzuwa, bakuma mujiba daga bakin Abie ko papi, dan aranarma ya koma inda ya fito, wannan dalilin Galadima ya samu yafara shirin komawarmu India da Zarar an kammala bikin Sauban daya rage sati biyu kacal. Ana saura kwana biyu d'aurin aure ya zauna da bayin ALLAH da suka hidimta masa akan su tanderu. Baffi, Baba Rabilu, Badi, Muftahu, Nuren, Saleem, Sir isa, su Ameer. Dukansu ya bisu da k'yauta ta girma, tare da musu godiya ta musamman mara iyaka, yakuma y'anta Badi tare da k'yautar muhallin zama mai nagarta a cikin masarauta, hakama sarkin mota, ya basu hak'uri bisa ga jinsa shiru, abaya tattalin arzik'insa ya raunana ne, koyace zai karramasu bashida k'arfin hakan, amma yanzu kam alhmdllh komai ya dai-daita. Suma sun masa godiya ta musamman a garesa da k'yak'yawar Addu'a, daga k'arshe ya kaisu ga Abie da Momma, sunci abincin rana tare da adalin tsohon Sarki wato Abie, sannan suka sha hira, dama kowa yasan Shiba mutum bane mai girman kai, ga yawan tsokana, shima yamusu k'ayuta ta musamman, hakama Momma tayi nata. Washe gari ana gobe d'aurin aure kenan da tashin hantsi yasakani shiryawa wai namasa rakiya wani waje. Kamar ko yaushe Sarkin Montane ke Jammu, yayinda dogaransa ke binmu a baya. Mun Isa wani waje kusada birnin gayu plaza, wajen ya had'u iyakar had'uwa, a da shagunane kawai a wajen, amma yanzu kamar an rushe anyi wani gini na musamman. An saka k'aton allo mai d'aukeda hotunan kayan gyaran gashi dana kwalliya, an rubuta *_LADIES MIRROR_* da manyan haruffa, hakama jikin k'ofar wajen dayasha glass, an saka babban allo a sama mai kawo wuta da d'aukewa, shima dai irin rubutun farkone a nan, wato *ladies mirror*, abin ya k'ayatar dani, yana rik'e da hannu na muka shiga. Ashe wajene na musamman na gyaran irin duk Wanda mace take buk'ata, gyaran jiki, saloon, kwalliya, kunshi, dakuma waje na musamman da kayan shafe-shafe na kwalliyar mata ake siyarwa, da glasses aka rarraba shagon, kowanne da 6angarensa, bayan ka fara iske reception a farko, sai office dayaji komai zam dake can k'arshen shagon, shima dai duk glass d'inne, amma daga ciki zagaye yake da labuloli, ba'a buk'atar ganin Wanda zai zauna a ciki kenan. Bayan mun gama zagaya ko ina muka Isa Office d'in, Galadima ya saka hannu ya yaye wani allo da aka lullu6e da farin k'yalle. Kallonsu nayi da mamaki, saiya nunamin rubutun jikin allon.. *_“Wannan tukuycine a gareki my mata, badan biyanki hidimar da kike daniba, dan idan biya zanyi abinda na mallaka kaf bazai iya biyankiba matata abar k'aunata, bugun zuciyata komaina Munaaya”._* Da tsantsar mamaki na d'ago ina kallonsa, yad'an ta6e baki da d'agamin kafad'a alamar gaskiyar kenan. Kawai jinai hawaye sun gangaromin, na fad'a jikinsa ina sakin wani kukan farin ciki. Hannu biyu ya saka ya rungumeni yana murmushi, sannan ya jani muka zauna bisa sofa guda d'aya dake a office d'in, ban tsaya wata-wataba na manna la66ana saman .....🤭. Caraf ya cafke tamkar dama jira yakeyi, gaba d'ayama mun manta a inda Muke, mun tsunduma duniyar masoya wad'anda suka soyu a soyayyarma, saida naji yana Neman kauce hanya sannan na dawo hayyacina. Na kuma rungumarsa tsam ina jero masa godiya wadda nama rasa wace iriya zanyi masa yasan naji dad'i. Ya rik'e fuskata cikin tafin hannunsa yana bina da kallo, “My mata babu godiya a tsakaninmu, inma akwaita to nine ya cancanci nayi miki, domin kinmin abubuwa da baki bazai iya lisafosuba, kedai kawai ki rik'eni Amana ni da yaranna da k'anensu masu zuwa, idan kinkai hakan kin gamawa Muhammad Sameer komai, na haramta miki yimin godiya inhar akan wannan d'an wajenne”. Ya kamo hannuna yana zaro key d'in mota a aljihu ya d'oran a hannu. Kallonsa nayi sannan na kalli hannayenmu, ya d'aga min gira da cije lips sannan ya mik'e. Tamkar sokuwa haka na bisa da kallo, gaban loka k'arama dake office d'in ya nufa, ya kwaso wasu file ya dawo inda ya barni tamkar wata gunki, d'ayan hannun nawa ya kamo yana d'oran files d'in, “Wannan sune bayanai da form na ma'aikatanki, angama d'aukar kwararru a kowanne fanni, wannan takardun wajene da kowanne lasisinsa, ko gobe kika shirya ma'aikata zasu fara aikinsu.................✍🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼 [8/21, 8:44 PM] 0mmer Farouk: *_Typing📲_* *_💡HASKE WRITERS ASSO...._* *_♦RAINA KAMA...!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* *_BOOK 3_* 👉🏻3⃣2⃣ *_🔚END!! 😢✋🏻_* ...............Ban San yanda zan musalta muku halin dana tsinci kainaba bisa ga wannan tukuyci na Galadima, saidaifa kafin wani dogon lokaci dukkan Wanda keda alak'a dani yasan da zaman wannan k'yauta, y'an uwa sai tayani murna sukeyi. Y'an gidanmu dai saida sukaji wannan bak'ar al'adar tasu ta hassada, amma sun d'an danne zukatansu sukaimin murna. Washe gari bayan d'aura auren Sauban da aunty mimi Galadima yaja gayyar abokansa da yayuna sukaje aka bud'e wajen saloon d'ina. Akuma ranar ma'aikata suka fara gudanar da aiki, dan a can naje na iske Galadima ni da tawa tawagar, na gana da dukkan ma'aikatana tare da basu umarnin duk Wanda ya shigo wajen a ranar amasa abinda yakeso k'yauta, Washe gari sai a fara na kudi. Bikin Sauban ya gudana cikin k'ayatarwa, itadai aunty mimi koda aka d'aura auren shikenan, tace wane biki kuma a shekarunta, ana gama shagalin na Sauban tareda amaryarsa Ni'imatullah d'iyar Mom da biyu, itama ta tare gidan mijinta professor Ibraheem Macid'o, musalta muku yanda mukasha shagali 6ata lokacine. Bayan bikin da kwana biyu Galadima ya fara koya min mota, koya motar da taso zama shiririta, wai dole saidai na zauna a cinyarsa ahaka za'a koyan, banida yanda na iya dole nayi hakan, cikin amincin ALLAH a sati biyu nagama kwarewa, kwana biyu da faruwar hakan na yaye su Amaturrahman bisa dagewar Ubansu akan shima k'annensu yakeso, danga Munubiya da ciki🤭🤣. Dole nayi wannan yaye yara suka koma wajen Momma. Kwanaki 10 cif dayin yayen saiga bak'ona yazo, karkuso kuga murna wajen Galadima, wai hanyar samuwar ciki ta bud'e. Ni dai shiru namasa ban tankaba. Randa kuwa nayi wanka ai babu d'aga k'afa, ALLAH mai iko da falala kuma ya amince masa, koda wata ya dawo babu jini babu alamarsa, hankalina ya tashi na birkice masa, sai yayta tuntsuramin dariya da fad'in “Yarinya an fad'a miki nid'in na wasane, zan zama Abbu a karo na biyu, ALLAH yasa su zama 3+3=6”. Tashinai nabar masa falon ina zun6ure-zun6ure, shikam yayta tuntsura dariya. Nima nayi farin ciki da samuwar cikin, tunda naga hakan shine burin mijina da farin cikinsa, sai kuma fatan ALLAH ya sauke mu lafiya, dan wannan karon dai mun sa6a ni da Munubiya. *_BAYAN WATA 6_* Cikina ya fito sosai, ina samun tattali da kulawar mijina, kai kace wannan shine cikin farko daza'a Haifa masa, ga shak'uwa mai yawa dake tsakaninsa da yaransa, abin akwai birgewa mai yawan gaske. Ranar wata juma'a kawai mukaga an tashi da wani gagarumin biki dabamusan na miye ba a masarautar, dama kusan kwanaki uku kenan bak'i nata sauka, ni dai harna kasa hak'uri na tambayi Galadima, yace, wlhy shima bai saniba. Ana sakkowa daga massalaci sallar juma'a aka hana Galadima shigowa gida, papi ya umarcesa da zuwa ya zauna inda aka tanada dominsa. Mamaki ya kamasa ganin gurin dank'am da jama'a, addu'a kawai aka gudanar papi yabada umarnin fara abinda ya tara mutane, daga baya koma mikenan jawabi zai biyo baya. An umarci Galadima da tasowa zuwa saman daddumar dasu Abie da manyan sarakuna ke zaune, ya zauna a tsakkiya shidai zuciyarsa na faman tsitstsinkewa da bugun mamaki. Turaki ya mik'e a tsanake zuwa gaban mai martaba Sarki Jalaludden Abubakar, yay gaisuwa tare da risinawa sannan ya zare rawanim dake kansa, gaba d'aga wajen aka d'auki kabbara, Abie yay k'asa da kansa yana share hawaye, shidai dan anfi k'arfinsane kawai, amma daba yanke wannan hukuncinba wlhy. tuni bugun zuciyar Galadima ya k'aru ganin Turaki ya nufo garesa, zaiyi maganar papi yay masa alamar yay shiru🤫. Dole ya maida bakinsa ya tsuke yana had'iyar yawu da k'yar. Tsohon Sarki Jalaludden ya taso da taimakonsa Turaki ya cire hular saman kan Galadima aka d'ora masa sabuwa dal, sannan aka fara nad'a masa rawani akai, jikin Galadima sai tsuma yakeyi, ya kafe papi da Abie da ido ko k'yaftawa bayayi, shikad'ai yasan a halin dayake ciki, zufa sai tsatstsafo masa take a kowacce mahudar gashi dake a jikinsa. Tsaf aka gama nad'a masa rawani jama'ar wajen suka d'auki kabbara, yayinda za'a saka masa alk'yabba sai dogarai suka baza riguna ana masa kirari. Galadima yay k'asa dakai idonsa na kwararar hawaye lokacin da kunuwansa ke jiyo masa jawabai daga bakin sank'ira. *_“ALLAH ya d'auki rawani ya maida bisa kan matashi kuma adali tsohon Galadima a yau yazama Sarkin wannan masarauta ta gagara badau bisaga adalcin tsohon Sarki mai murabus a yau, masarautar gagara badau tayi sabuwar amarya, a halin yanzu Mai martaba Muhammad Sameer Saifudden Abubakar shine Sarkin wannan adalar masarauta, ALLAH ya tayashi rik'o, yabashi ikon koyi da k'yawawan halaye irinna manyan wannan gida”._* Tuni waje ya harmutse da surutai, kowa na fad'in albarkacin bakinsa. Galadima kam saida papi ya rungumesa a jikinsa sannan yafara samun nutsuwa, yayinda aka kawo Matawalle shima aka zaunar aka nad'a masa rawanin wazirci, shine zai zama wazirin d'an uwansa Sarki Muhammad Sameer Saifudden Abubakar. Ai tuni guri ya rinca6e, babu maijin zancen wani, kafafen yad'a labarai da social media duksun d'auka, masu murna nayi masu bak'in cikin nayi, (kusan shigabanci, dolene kasamu masoya da mak'iya😭). Mama Fulani da labarin ya Isar mata zarewa tayi, sai surutai take Wanda ba kowa ke fahimtaba, Gimbiya zulfah kuwa yanke jiki tayi ta fad'i wanwar, koda aka zuba mata ruwa ta farfad'o saita kama aman jini zuciyarta yariga ya buga. Ba'a katse su papi daga abinda sukeba aka nemo doctor dazai dubata, saidai bata d'auki wani dogon lokaci ba tare ga garinku nan. Haka duniya take, lokacin da wani ke zuwa sannan wani ke ficewa, hakanne ga gimbiya Zulfah, tatafi a randa Galadima ya zama Sarkin gagara badau.🤴🏿😝😁👍🏻 Ni kaina da labarin zaman mijina Sarki yau babu zato ya zomin saina rikice, na rud'e, ganin lamarin nake tamkar tatsuniya ko mafarki, ga ciki, nama rasa murna zanyo ko kuka. Ban fita a wannan magaginba saiga zancen halin da gimbiya zulfah take itada mama Fulani, saikuma ga abinda ya girgiza kowa shine mutuwarta. ********* Koda aka buk'aci jawabi daga bakin Galadima kasawa yayi, shifa ganima yake a mafarki komai ke faruwa, shima Matawalle ya kasa cewa komai, sai zirar da hawaye kawai sukeyi Wanda hakan ya birge kowa da bada mamaki. Abubuwa sun rinca6e fiye da yanda bakwa zato a masarautar gagara badau, bayan an sallaci gawar gimbiya zulfah aka kaita makawancinta na gaskiya y'ay'anta na kuka da y'an uwanta. Kiri-k'iri ganin mijina ya gagareni har dare, Abdurraheem sakin k'ulafucin Uba sai kuka yake yak'iyin barci, su Amaturrahman da sukayi nasu na lallashesu sai suka kwanta, dan sunsaba da yayi sallar isha'i yana tare dasu, amma yau shiru babu amo babu labari. Nikam sainaji abin yana cizon zuciyata, indai wannan mulki zaisa mijina yin nesa dani bana farin ciki, saigani da kuka rurus. Sai misalin 12pm Sarki Muhammad Sameer yasamu rakkiyar zuwa sashenmu. Ina zaune afalo nayi tagumi naji alamar mutum tsaye a kaina. A firgice na d'ago kaina ganin mijina saina mik'e a firgice tare da fad'awa jikinsa na saki kuka. Shima rungumeni yayi sosai yana sakin nasa kukan, sannan ya d'aukeni cak zuwa cikin bedroom d'in ya ajiyeni a saman gadon, kuma rungume juna mukayi muna cigaba da kukan mu. Tsawon lokaci muna haka, sannan yafara dakatar da nashi yana lallashina. “Munaya kinga abinda su papi sukaimin ko, ni dai banason sarautarnan, amma sunk'i saurarena, wlhy banaso munaya, banaso nidai”.... Yakuma fashewa da kuka. Tausayinsa saiya kuma kamani, nakuma rungumesa tsam a jikina, abinda kaga ya saka Galadima kuka aiba k'arami beneba kuwa. Daure zuciyata nayi na shiga lallashinsa. Na kuma rungume sa sosai cikin nutsuwa ina fad'in, “Mijina ba komai ne ake tuntu6e dashi bisa shiryawa kaiba, wani abun tunkan kasan tuwarmu gudan tsoka rubutaccene a littafin k'addararmu, babu wani d'an Adam da alk'alamin k'addararsa ke a tafin hannunsa, gudun zuciya yafi na k'afafu sauri, idone kawai ke iya banbance fari da bak'i, baki kuwa d'and'ano kawai yake tantancewa, aikin kunne kuwa jine kawai da banbance k'arar sauti, baka tunanin duk mutum mai baiwa ALLAH ke ba damar banbancewar? Irinku kune kuka cancanci mulkin al'umma, domin kuwa bashine burinku ko damuwarkuba, kune zaku iya adalci da tausayin na k'asa daku, ka amince dayin wannan sadaukarwar ga iyayenka da al'ummarka, domin samun damar k'ar6ar sakamakonka wajen adalin Sarki mai tarin rahma da jin k'ai. Zuciya da tunani duk mallakar gangar jikice, haka gudanar jini da motsin ga6o6i, su papi sune sukasan tayaya ka cancanta kaida d'an uwanka, har suka d'auki wannan nauyin suka d'ora muku, Ku kar6i yau d'unku da hannu biyu, domin jiyanku tazama labari, Ku hidimtawa gobenku domin Ku ribantu da jibinku, wannan shine kawai masalaha mai k'ayatarwa ga mu ahalinku, masu ganin baka kaiba saisu ajiye makamansu su tabbatar da ka kai d'in, kazama RAINA KAMA mijina, kosu amince, ko karsu amince kaine RAINA KAMA”. Tsam ya rungumeni yana fad'in “kece RAINA KAMA munaya, domin a dalilinki ne suke ganin nayi feeling, har ake ambaton ni da sarauta har Abadan, su ganin auren talaka shine k'ask'anci, shine ke nufin ka koma k'asa, a yak'ininsu saika auri y'ar wani mashahurin Sarki ne darajarka ke a idonsu, sun manta ba talaucine ya rarrabe tsakaninmu ba, Wanda yafi wani bautar ALLAH shine mafifici a cikin bayi, su Papi sun tabbatar min kina d'aya daga cikin manufofinsu na bani Sarauta, sunason tabbatarma duniya da mai sarauta zai iya auren d'iyar talakawa, basai y'ar mai mulki irinsaba, sunason duniya tasan shima talaka akwai baiwa da darajar da ALLAH yamasa fiye da mai mulki, sunason duniya tasan ba mai mulki bane mafi k'ololuwar daraja a cikin bayi, kowanne Bawa da tarin daraja da baiwar da ALLAH ya masa, kinga kuwa kece RAINA KAMA my heartbeat, ko ni kin zamemin RAINA KAMA balle su da suke tunani ba daidaiba”. Kasa magana nayi, muka rungume juna tsam cikeda so da k'auna. An cigaba da gudanar da gagarumin biki na wannan nad'in sarauta, kwanaki 5 cif akayi anayi, danma mutuwar gimbiya zulfah ya rage armashin bikin. bayan lafawar komai da sati biyu mukaje India Galadima ya maida dukkan harkokinsa nacan ga Sauban daya zama tilas ya d'auki matarsa su koma can, dole kuma ya ajiye aikinsa duk da sonsa da yake, su Vijay zasu cigaba da kulawa da komai, idanma suna buk'atarsa zai cigaba da kawo shawarwari. Mun dawo da kwanaki biyu aka gama kammala aikin Company d'insu na nan Nigeria, Wanda dole su Vijay sukazo suka aiwatar da komai, zuba masa kaya da d'aukar ma'aikata da dukkan abinda yakamata ayi. Wata d'aya cif a tsakani aka basa umarnin shirya fara gudanar da mulki, Shiga fada da nad'e-nad'en sarautu da zaiyi, dakuma Neman matar aure dazai k'ara.🤦🏻‍♀ Wannanfa Abu ya tayarmin da hankali sosai, ga cikina ya tsufa, aiko na birkice masa naita kuka, kai wlhy kishiya da ciwo, duk dauriyarka saikaji babu dad'i, musamman idan kana son mijinka kuma. ALLAH Sarki Momma Uwa ta gari, itace taita kwantarmin da hankali da kalamai masu sanyaya zuciya, hakama Galadima yayta lallashina da nunamin muhimmancin lafiyata kodan tsohon cikin dake jikina, itama Munubiya da Innarmu haka, nima da naga mijina da kowa na son ganin kwanciyar hankalina saina kwantar d'in, na kar6a k'addarata da hannu biyu. Da farko d'iyar Mom akace ya aura, bankuma San yanda akayi ya zameba yace yabani wuk'a da nama na za6o masa dukkan wadda tamin, koya take wlhy zai aura shikuma. Kusan sati biyu daya bani sainaita nazari da hasashen wazan za6a masan, haka kawai matashiyar budurwa Hafsat da muka ta6a had'uwa a jirgi ta fad'omin a rai, lokacin inada cikinsu Amaturrahman, tamin wani taimako da Galadima ya yaba mata sosai, Wanda harna kamashi yana satar kallonta, amma a time d'in saiya basar kamar yanda halayyar tasa take, Nima sai banja maganarba, mukan gaisa da Hafsat miss xoxo time to time, amma mun dad'e bamu had'uba, inagama tun taron sunan su Abdurrahman da tazo. Muna zaune dashi na lalubo hotonta da mukayi ranar suna tare na nuna masa. “My king wannan ta makane?”. Kar6ar Hoton yay yana kallo, yay wata irin zabura yana ajiye hoton gefe da hararata, “Kina zargin ina sontane komi?”. Murmushi nayi ina d'auke hoton, nace, “yanayinka da amsarka kawai ta wadatar dani ranka ya dad'e, danason ma kanason miss xoxo da tuni na had'a wannan alak'ar wlhy, ALLAH yabamu zaman lafiya”. Duk yanda yaso bijirewa da nuna ba haka bane ban sauraresaba, na nunama Momma photo aka shiga binciken miss xoxo. A cikin sati biyu aka gama komai, duk da itama ta nunamin bata aminceba. Duk da kishi na cina haka na jajirce tsakanin borensu, babu 6ata lokaci akasha biki. Da kaina namata rakkiya d'akin mijinta a maimakon rakkiyar jakadiya da har yau bai za6aba., nai k'ok'arin danne kishina nai mana addu'ar zaman lafiya. Na dawo d'aki ina kuka da rungume y'ay'ana, akuma asubahin farko na farka da nak'uda. Wadda har aka wuce dani asibiti Sarki Muhammad Sameer bai fitoba, yanacan yana lallashin amaryarsa daya maida cikakkiyar mace a daren jiya. Na sauka lafiya na haifi d'a namiji mai kama dani sak, sai daga baya labari ke kaiwa kunnen Sarki Muhammad Sameer, ya rikice da murna, gashi babu damar binmu a asibiti, dole ya hak'ura har muka dawo. Fad'an farin cikin samun wannan haihuwa ga Sarki 6ata lokacine, hakama su Abie da tsohon Sarki da a yanzu suka koma daga gefe suna koyama yaransu dabarun mulki. Washe garin suna kuma Sarki Muhammad Sameer ya zauna a fada, tare da yin wasu nad'e-nad'e, hardasu Badi a ciki, sarkin mota da Sarki k'ofa sunce iya wuya suna tare dashi. Haihuwar danayi Ce ta d'auke hankalina daga damuwar kishin mijina da wata, duk da bana nuna kishin dama a fuska balle Hafsat ta fahimta, dan Alhmdllh tarbiyyarta tasa muke zaune lafiya, saima k'ok'arin jan yarana da take a jikinta, yarona yaci suna Abdul-fatah, papi kenan, daga Hafsat kuma Sarki Muhammad Sameer yace ya tsaya, mata biyu sun ishesa, ALLAH yamusu zaman lafiya. Rayuwa ta cigaba da gudana cikin nasarori, wajen saloon d'ina nata ha6aka, da kud'in shigarsa na d'auke kaso mafi tsoka na nauyin gidanmu, mahaifina ma yasamu sarauta da Sarki Muhammad Sameer ya nad'ashi, hakan yamin dad'i sosai. Munubiya itace mai kula da ladies mirror, office d'inma ita ke zamansa time to time, danni banida wannan damar a yanzu, fitarma sai wadda ta zama tilas nakeyi. Sarki Muhammad Sameer nada watanni takwas akan mulki ALLAH yayma mama Fulani rasuwa, tsakaninta da papi wata 1, wannan rasuwa biyu ta matuk'ar girgizamu, dan Sarki Muhammad Sameer kusan zarewa yayi akan mutuwar papi, yabasa gudunmawa mai yawa a rayuwarsa, wadda mantata abune mai matuk'ar wahala a garesa, mai makon babansu Nuren ya hau mulkin, sai yasa aka nad'a Nuren d'in. Sarki Nureddin ALLAH ya tayaku ruk'o baki d'aya. Babu dad'e da nad'im Sarki Nureddin akasha shagalin bikin Saleem da Feena, bikin dayay armashi sosai, dan itace last mace dasu innarmu zasu aurar, saura y'an k'ananun y'ay'ansu Aryaan, Aiyaan da Ahmad, Wanda a yanzu sun zama samari masha ALLAH, dan duk suna sa2 a secondary school, jirama Sarki Muhammad Sameer yake su kammala ya had'asu da Khaleel su wuce karatu. A yau kuma Munubiya ta kawo mana ciyara da y'ay'anta Meenal, Ameen da k'aramar Ai'sha muna ce mata Islam. Munsha hira sosai, taita mamakin yanda nake zuba mulkina, yo matar Sarki uwar gida wasace😂👍🏻🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀. *_BAYAN WASU SHEKARU_* Rayuwa ta shud'a ababen dariya Dana kuka sun faru iri-iri, an haifi wasu wasu sun rasu, hak'urin zama Na yau da kullum, wataran a 6ata ma koka 6atama wani. Zuwa yanzu kam munyi rashin wasu daga cikin iyaye y'an uwa zuwa kakanni, ALLAH yayma Abbanmu rasuwa shida wasu matan gidanmu biyu, inno ma haka, yayinda innarmu ta gama takaba sai danginsu sukazo suka tattarata zuwa k'asarta ta haihuwa, muna kuka tanayi hakama jama'ar gidanmu da y'an anguwa, Dan bamason tafiyar tata, amma hakan gatane a gareta komawa cikin ahalinta, a gagara badauma kam mun rasa da yawa, tsohon Sarki jalaludden Abubakar ALLAH ya masa rasuwa sakamakon ciwon hanta, wadda ya dad'e da ita a jiki Ashe, wannan ma shine dalilinsa na dagewa akan Abie ya kar6a mulki. Saida rayuwa tazo gangara yake sanar ma Abie d'in Wanda shima zuwa yanzu girma ya kamashi sosai, Dan yatsufa komai ma sai an masa, danma ALLAH yabashi gwarzuwar mata Momma, dukda itama girman ya kamata bata gajiyawa da hidimarsa. Sarki Muhammad Sameer Saifudden Abubakar, adalin Sarki da talakawa ke alfahari da mulkinsa, musamman ma matasa da akullum cikin bin hanyoyin inganta rayuwarsu yake, suna zaune lafiya shida wazirinsa kuma d'an uwansa, babu wani y'an ubanci ko k'iyayyar juna, k'yawawan zukatansu sun sakasu kawo canji mai yawa a wannan masarauta, da farko su Talba ne sukaso kawo musu hargitsi, tunda suka fahimci haka sai aka sakasu barin k'asar tilas suda iyalansu, tun daga nan masarauta tadawo dai-dai. 6angaren Harun ma ya fito tun lokacin daya cika shekaru goma, amma bisaga karamci Na adalin Sarki Muhammad Sameer saiyasa aka kawosa fada, yay masa hidima mai yawa, wadda ta sakashi kuka da gurfana gaban Sarki Muhammad Sameer Neman gafara da nadama akan abinda ya aikata, Muftahu da ayanzu yake rik'e da sarautar matawalle yay murmushi yanama Sarki Muhammad Sameer magana da ido akan ya yafe masa tunda yayi laushi, Sarki Muhammad Sameer ya jinjina kansa yana murmushin nan nasa Na k'asaita da cizar lips. Yafewar da Sarki yamasa Ce tabashi damar Neman gafara ga Uwargida Sarauniya Munaya itama, babu wani ja'inja tace ta yafe, ba'a barsa ya zauna masarauta ba, anmasa hidima mai yawa da aure aka sakashi komawa wata k'asa, Dan bawai kowa ya gamsu da tuban nasaba, ayanzu kuma Sarki da wazirinsa basa buk'atar duk wani mai ru6a66iyar zuciya a kusa dasu. Sarauniya Munaya uwargidan sarki mai fad'a aji a wannan masarauta, jarumar mace mai nagartacciyar zuciya, hamshak'iya wadda ayanzu tazama babbar mace jerin manyan mata sahun faro wajen dattako da mulki dama dukiyar itada y'ar uwarta Munubiya. A yanzu yaranta takwas a duniya, Amaturrahman, Abdurrahman, Abdurraheem, Abdul-fatah, Ai'sha, Zeenah, Saifudden, jalaludden Auta kenan, Ai'sha da Zeenah da suke kira da Safah da marwah tagwayene, bayan haihuwar Abdul-fatah tayisu suma, daga nan sai mai sunan Abie, dakuma auta takwaran tsohon Sarki babansu matawalle konace waziri, ayanzu kam duk sunzama manya, musamman su Amaturrahman da suke manya duk suna a jami'a, suna k'asar India tareda uncle d'insu Sauban da ayanzu shima yazama babban mutum, yazama babban d'an kasuwa bisaga jagorancin dukiyar d'an uwansa, yayinda su Aiyaan da Khaleel, Aryaan, Ahmad ke taimaka masa, kaga matasan samari abokan juna kenan, kansu ahad'e yake su hud'unnan, sune yanzu duniya ke yayi take son gani a fanin na'ura mai kwakwalwa wato Computer, Wanda ayanzu Abdurraheem da Abdurrahman suke k'ok'arin dannesu, Dan matasan samarin biyu sun zama magada kwakwalwa irinta mahaifinsu Sarki Muhammad Sameer suma. Itama Hafsat yaranta hud'u, biyu mata biyu maza, wad'anda duk suka taso a hannun Munaya, akwai zaman lafiya da k'aunar juna tsakanin Hafsat da Munaya mai birgewa, Wanda ya kawoma Sarki Muhammad Sameer kwanciyar hankali da k'yautata musu gwargwadon k'arfinsa, kamar yanda suma suke k'yautata masa da dukkan iyawarsu. Yaran Munubiya itama 6, Dan itama 8 d'inne ta haifi biyu babu rai, Ameen yana tare dasu Abdurraheem, yayinda meenal takanyi Rabin rayuwartane a masarautar gagara badau, saboda batada k'awa wadda tawuce Amaturrahman. Inhar basa Masarauta to sunacan gidansu meenal d'in, sun zama y'an mata ababen birgewa, ita meenal tana masifar son Abdurraheem ne shikuma k'asaita da muskilanci irinna ubansa Sarki Muhammad Sameer tariga tazama jinin jikinsa, yata basar da ita kenan, wannan Abu Na cimata rai, amma aduk sanda ciwonsa zai tashi tafi kowa shiga damuwa, idan kuma taga yanda Ameen da Amaturrahman ke soyewarsu saita kumajin kanta a damuwa, shikam Abdurrahman Niger ya tsallaka, Dan d'iyar Sarki Issifa da Sarauniya Ayusher Rabi'a (Amatullah) yakeso da k'auna, ya rikice sosai, haka kawai saiyayi shiri wai yatafi yima Inna Hutu, nanko wajen Amatullah yaje. Wannan hutune Na k'arshen shekara daya kasance duk yaran suna Nigeria, saboda bikin su Aryaan da akasha babu dad'ewa. Sarauniya Munaya kishingid'e a kilisarta hadimanta nata hidima a gareta, matasan samarin y'ay'anta suka nemi ison shigowa gareta. Izini ta basu, tareda sallamar dukkan Hadimanta. Abdurraheem da Abdurrahman suka shigo, Kansu d'aya, kamanninsu d'aya, halayyace kawai ta banbantasu, Abdurraheem halin Sarki Muhammad Sameer ne gaba d'a a jininsa, yayinda Abdurrahman yazama mai irin halayyar Uncle Sauban da Abie. Har suka zauna idonta Na kansu, sukai zama irinna k'asaita suna gaisheda mahaifiyar tasu. Fuskar Sarauniya Munaya d'auke da Murmushi ta amsa, takai dubanta ga Abdurraheem dashi ko kad'an bashida yawan magana. “Abdurraheem saunawa zan maka magana akan aske sumarnan ne?”. Lips d'insa ya cije (d'an gado kenan😂) yanad'an 6ata fuska. “A gafarceni Ummu, wlhy zan Aske, jiya nafita zanje shagonki askin sai takawa yayi kirana ya Sani wani aikin, amma Ummu shima Abdurrahman kimasa magana ya yanke wannan k'umbar, ALLAH k'yank'yaminta nake.......” Harara Abdurrahman ya zuba masa, zaiyi magana Sarauniya Munaya ta katseshi tana tashi zaune, “Abdurrahman naga hannunka”. “Ummu karki yarda da gulmar yaronnan ALLAH, yatsa biyunefa”. Ya k'are maganar da kuma harar Abdurraheem daya ta6e baki ya cije lips. Sarauniya Munaya tace, “Yimani shiru, nabaku nanda dare wlhy kowa ya cire k'azantar jikinsa, ina kuma fata anje an bama Abie magungunansa?”. “Eh Ummu, Abdul-fatah ya bashi, yanzuma daga sashensu muke barci yakeyi, amma su Amaturrahman nacan sun cikama Momma kunne da surutunsu Na tsiya itada Meenal”. Murmushi Munaya tayi, Dan ita babu abinda take gani tattare da Abdurraheem sai Mijinta, shikuma Abdurrahman rashin iya R kawai ya gado shida Safah da Marwah duk basu iya R ba, to ga Saifudden nanma akwai k'asaita tsiya, d'an k'arami dashi sai mulkin tsiya, ga jarabar son girma, bawani girman jalaludden yayiba amma inkaga yanda yake basa umarni saikaci dariya, hakama yaran Hafsat. Sarauniya Munaya tacigaba da hira da yaranta da musu nasihar tsare mutuncin Kansu kamar yanda ta saba. Wayarta da sak'o ya shigo ta d'auka tana dubawa. Sarkine da kansa. *_Gaskiya ina buk'atar jin d'umin my mata._* Murmushi Sarauniya Munaya tayi tana kallonsu Abdurraheem da suka satar kallonta, idan kaga irin wannan murmushi ga mahaifiyarsu to akan Abbun sune kawai. Tad'an hararesu tana fad'in “Takawa ba yana fada ba?”. “A'a yana turakarsa, Dan zamu shigo nan mukaga fitowarsa daga fada”. Nanma murmusawa Munaya tayi kawai, ta tashi zaune tana gyara zaman alk'yabbarta, “Kuje Sweetheart Na nemanku, amma Ku dawofa da wuri, kunsan yau ranace ta musamman da takawa ke zaman hira damu, karkuyi sakacin dazata wuceku, akwai sak'o a d'akina saman mirror Ku d'auka akai mata, zan kirata namata bayani”. A tare suka amsa da to Ummu. Ta mik'e ta shiga bedroom d'inta, mintuna kusan biyar saigata ta fito tabi wata hanya da zata sadata da sashen Sarki Muhammad Sameer kai tsaye batare da kowa ya gantaba, wannan tsarinsane, Dan baya buk'atar wata jakadiya a tsakaninsa da matansa, yace suke rura munafunci a tsakanin matan Sarki. Kallon juna Abdurraheem da Abdurrahman sukai, sukayi murmushi tareda tafawa, soyayyar iyayensu Na masifar kashesu, burinsu shine suyi koyi, tafawa sukayi sannan suka mik'e domin cika umarnin Na zuwa wajen gwaggonsu Munubiya, Dan ita kad'ai ummunsu take kira da Sweetheart. Sarki Muhammad Sameer Na kishin gid'e a k'ayataccen falonsa dayaji kayan more rayuwa, lap-top yake sarrafawa hankalinsa kwance, sai tataccen ruwan tuffa dake ajiye a gefensa, k'amshin matarsa gimbiyarsa komansa da yajine ya sakashi d'ago k'yawawan idanunsa yana kallon k'ofa tareda amsa mata sallamarta yana zare medical eyeglasses d'in idonsa. Tunda ta shigo ya dakata da danna lap-top d'in ya zuba mata ido kawai, cikeda tafiyar k'asaita ta isassun mata ta k'araso gareshi. Zata zauna gefe ya kamo hanunta yana tashi zaune sosai ta zauna saman cinyarsa, su duka ajiyar zuciya suka saki, ya sark'e idanunsu a waje d'aya yana mata murmushin da ita kad'ai take samun ganinsa a fuskarsa, cikin matso da fuskarsa gab da tata ya hura mata iska tafara farfar da idanu. Lumshe idonsa yayi yana cijar lips, a hankali ya furta I love you my Queen, my Everything? ”. “i love you too my king”. Munaya tafad'a a hankali itama cikeda salo. Bashida za6in daya wuce had'e bakinsu, dukda girma ya kamasu harda manyan y'ay'a da zasu iya aurarwa soyayyarsu bata tsufaba, tun anayi a afalo harya d'auka abarsa suka shige bedroom. Bayan wasu y'an lokuta suka fito wanka fuskarsa kowanne d'auke da murmushi, Munaya ta kalli mijinta cikeda so da k'auna. “My king miya faru kabaro fada da wuri haka?”. Murmushi Yamata mai saka zuciya nutsuwa, ya zauna kusa da ita yana kwantota jikinsa, cikin magana rad'a yace, “kewarkice kawai, jinai bama Na fahimtar komai da ake a fadancin, sai gizo kikemin kawai, shiyyasa Na buk'aci shigowa Na huta, bagashi Na huta d'inba?”. Yay maganar cikin d'age gira d'aya da kashe min ido d'aya”. Murmushi nasaki ina kuma shigewa jikinsa, nace “Anya kuwa a tarihin masarautar nan anta6a Sarki irinka?”. Murmushi Sarki Muhammad Sameer yayi yana d'ago fuskarta da sark'e idanunsa cikin nawa, “miyasa kika fad'i haka?”. Murmushi nima nayi ina shafa k'irjinsa, “Kaine Sarki Na farko dakan gana da iyalansa aduk lokacin da yaso, babu maganar jiran dare, kaine Sarki Na farko dakan ware wasu ranaku Dan zaman hira da dukkan iyalansa kawai amatsayi Na Uba ba sarkiba, lamarinka akwai k'ayatarwa yalla6ai”. Hararta yayi dajan hancina, “bazaki manta da sunannan ba ko?”. Dariya mai d'aukar hankali nayi ina fad'in, “kaida sunanka, yalla6ai Na yalla6iyarsa”. Shima dariyar yayi yana kuma rungumeni a jikinsa, “Wlhy kin zuba rashin ji sosai My mata, bak'aramar wahala nashaba lokacin auren Contract d'in nan, naga alamar tsiwarki Safah ta gado gaba d'aya, yarinyarnan batada tsoro ko kad'an, ga iya magana, tafi Marwah wayo sosai”. “Ai Marwah miskilanci da gatan da Hafsat ke musune ke d'awainiya da ita kawai, yarinyarnan miskilancinka ta gado itama, itada Abdurraheem da Saifudden da Khadeeja (d'iyar Hafsat) wlhy duk hallayarkace, rashin son hayaniya, miskilanci, k'asaita da basar da Abu tamkar bai damesuba, rashin iya r, ga salon cizar lips irin naka da Abdurraheem keyi shida auta jalaludden, nifa saidai naita kallonsu idan sunayi, Dan kai nake hangowa gaba d'aya a zamanin k'uruciya, musamman Abdurraheem ”. Sarki Muhammad Sameer yay murmushi da sumbatar goshina, a hankali yace, “my mata k'yan d'a......?”. Nace, “yagaji ubansa”. Yace “kin gama magana Sarauniyar sarakuna, time d'in barci yayi”. Bai barni nak'ara maganaba ya jani saman gadon tareda ja mana bargo mara nauyi. Har barci ya kwashesa ni nakasa nawa, Na zuba masa idanu ina tuna abubuwa masu yawan gaske da suka faru a tsawon shekaru 25 da aurenmu, Galadimana Muhammad Sameer yanzu yazama Sarki Muhammad Sameer, mutum mai tarin k'asaita, mulki, k'yawawan halaye masu nagarta, hak'uri, kawaici, dattako, iya zama da mutane, tausayin Na k'asa da shi, k'yauta da k'ok'arin tsare gaskiya, wad'annan duk halayyarsace dake kuma k'aramin k'aunarsa da addu'ar y'ay'anmu koyi dashi, Na matsar da fuskata kad'an ina manna masa Sumba a la66a, yad'an bud'e ido yamin murmushi dakuma sanyani a jikinsa. Daga nan nima barcin yay awon gaba dani. Sai bayan sallar la'asar sakaliya Na baro sashen Takawa, nafito sainaji sha'awar lek'a Hafsat, Dan duk yau bamuga junaba saboda tayi bak'i a yammacin jiya, tsakaninmu ma akwai k'ofar dake sadamu da juna batareda rakkiyar kuyangi ba, saidai abinda yasaka jikina sanyaya iske Hafsat a k'aramin falonta tareda bak'inta suna zugata akan zamanmu, ta mik'e tsaye karta yarda Na cigaba da mulkarta, kowa yasan nama fi sarkin mulki, Dan sai abinda nace yakeyi koda a fada, itako tazama tamkar wata sa d'akarsa. Fushin daya tasominne yasani daka musu tsawa. Bilyn Abdull da Hafsat suka rikice, ko kad'an basusan da zuwan Sarauniya Munaya falonba, hakama Maman kadee da Aysha DanSabo da Rano, party zarah, Ummu Basheer, khaleesat hydar, Ummi Ai'sha, Faxy fashion, Zee Bawa, zee Yabour, Ayusher Muh'd, Mamugee, Asmy b Aliyu, Silmzy, Feedohm, Bily galadanci, Safiyya Huguma, kdeey duksun rud'e, Dan dama sune bak'in Na Hafsat miss xoxo. Hafsat ta mik'e tana nufar Sarauniya Munaya datayi fushi zata fita, “Please gimbiya ki saurareni, ko kad'an niban d'auki zugarsuba, dama jira nake su gama Na kora musu bayanin bakina”. Jin wannan magana sai Sarauniya Munaya ta tsaya cak, sannan ta juyo da baya tana danne fushinta da maye gurbinsa da murmushi. Dawowa tayi ta zauna duk tana kallonmu, cikin sanyin murya tace, “kunason sanin yanda aikai nasamu dukkan fada da matsayi a zuciyar mijina Sarki Muhammad Sameer fiyeda kowacce mace bayan mahaifiyarsa?”. A tare suka amsa da eh. Tai murmushi da zame hular alk'yabbarta tayi baya, sannan ta kuma gyara zama da nutsuwar maida dukkan hankalinta garemu tafara bamu labari tun daga kan harmutsi da halayyar gidansu zuwa yanzu damuke tare da ita a yanzun. Wannan shine mak'asudin fitowar labarin RAINA KAMA ga sauran Fan's. Gaba d'aya sai jikinmu yay sanyi, domin labarin ya girgizamu, Sarauniya Munaya ta cancanci fiyema da hakan ga Sarki Muhammad Sameer Saifudden Abubakar, babu abinda zamuce saidai binta da fatan alkairi, itama k'awarmu Hafsat miss xoxo mu bita da addu'ar samun k'auna ta musamman a zuciyar Sarki Muhammad Sameer, dukda itama Alhmdllh tana samun dukkan kulawa a garesa. Mun bama Sarauniya Munaya hak'uri da Neman yafiyarta akan jahiltar abinda bamu saniba, lallai idan kaga mace Na mulkin gidanta karka zargeta, Dan bakowacce bace take zama Sarauniya a gidan miji bisaga bigiren kauce hanya, wata k'yawawan hallayartane suka siyamata wannan matsayin da girman da soyyar ga mijin da ahalinsa, domin ayau labarin Munaya ya tabbatar mana da haka, hardajin sha'awar kasantuwa masu koyi da k'yawawan halayyarta. _Mun yarda lallai Mahaifansu Munaya Inna da mama Rabi'a *RAINA KAMA* ne, Galadima, kuma a yanzu Sarki Muhammad Sameer shima *RAINA KAMA* ne, Munaya & Munubiya suma *RAINA KAMA*, Momma *RAINA KAMA*. Abie *RAINA KAMA*, kai jama'a dayawa a wannan labarin sun zama *RAINA KAMA KAGA GAYYA!!*_ 😁👍🏻 Atake a wajen tace ta yafe mana, takuma gayyacemu zuwa sashenta inda tasa aka had'a mana beta ta musamman😋😋, dazan Baku labarin garar arzik'i da abinda wad'anan guys d'in Na HASKE sukayi dakunsha dariya, saidai ina tsoron suburbud'a alk'ur'an🤣🤣⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Abin kallo bai k'are manaba sai da daddare, bayan sallar isha'i kai tsaye sashen Sarauniya Munaya akayo masa rakkiya, Dan wannan rana tana cikin ranakun dayakan kasance da iyalansa ba a matsayin sarkiba, matsayin miji ga matansa, sannan uba ga y'ay'ansa. Yanda ya zauna yana wasa da dariya dasu, kowa Na k'ok'arin fad'ar abinda ke bakinsa, yayinda matansa suka sakashi tsakkiya da yaran 12 cif, k'ananun duk suka a jikinsa kowa farincikin ganin Abbu Na tare dashi, sunci sunsha a tare, zuwa k'arfe 10 suka d'unguma sashen su Momma, acanma hirar ta gudana mai cikeda farin ciki ga wannan ahali, murmushi ya Gaza d'aukewa a fuskokinsu, kowanne yanajin tsantsar so da k'aunar junansu a cikin jininsa da ayukansa..........✍🏻🔚 Kamar yanda Nina k'aunarku da kewarku ta mamayeni a lokaci d'aya😭. Tammat bi hamdullah. *_Na godema Ubangijin al'arshi daya horemin dama da kwarin gwiwar kai wannan labari k'arshe dayay ta tafiyar hawainiya tamkar bazai k'areba😁, kuskuren danayi ALLAH ya yafemin, abinda Na fad'a dai-dai ALLAH ya taramu a ladan Baki d'aya, bakina bashida Kalmar furtawa agareku masoyana, kun nunamin d'unbin k'auna da soyayya akan wannan labari, ina rok'on ubangiji ya amfanar damu da alkairan dake cikinsa, kuskuren kuma mu watsar dashi gefe domin girman ALLAH, Dan kunsan d'an Adam azijine, Nina ina a layinsu ni bilyn Abdull, ALLAH kabamu ikon koyi da k'yak'yk'yawa, ya nisantamu daga mummuna, ALLAH yasa munada Rabin sake had'uwa a buk Na gaba.😭🙏🏼_* _ALLAH ka gafartama mahaifina, kakai rahma da Ni'ima kabarinsa, ka azurtashi da yalwatacciyar rahman tareda dukkan sauran y'an uwa musulmai da suka kwanta dama😭🙏🏼._ _ina Neman afuwa ga dukkan Wanda Na 6atamawa a yayin rubuta wannan littafi da Sanina ko'a rashin sani, Nima Na yafema duk Wanda ya 6atamin, ALLAH ya yafe mana Baki d'aya._😭🙏🏼 *_Akwai kuskuren danayi a salon wannan labari, domin kusan Munaya ke bada labarin ga k'awayen miss xoxo, amma mantuwa kansani shiga ciki, hakan tafaru bisa d'an rikicewa bayan dawowata daga hutun azumi, ina fatan zakumin afuwa, kuma zakuga gyara anan gaba insha ALLAH, domin wani lokacin gazawama nasarace, saika Gaza kake d'aukar hanyar gyara, ALLAH ya ganar damu baki d'aya, Rufaida Umar ina godiya sosai, Dan kece kika farkar dani kafin kowa_*😊😘😘👍🏻 Takuce sai *_BILKEESA IBRAHEEM MUSA_* _(Bilyn Abdull😉👌🏻)_ ALLAH ya sake had'amu da alkairinsa.😁🙏🏼 I love you wijiga-wujiga, mazga-mazga, manya-manya, irin trillions d'inan my sweet fans😘😘😘😘😘😘❤❤❤❤❤❤😁👍🏻. I miss you wlhy✋🏻😭 *_SANARWA_* _Yakamata y'an uwana musulmi mu farga wajen yawan binciken lafiyarmu akai-akai, Dan cutar ciwon HANTA ta yad'u a cikinmu sosai, gashi mafi yawanmu bamu saniba😭, sai taci k'arfinmu muke farga saboda bamuda yawan kulawa Na binciken lafiya sai ciwo ya kwantar damu, gashi anata d'aukar ciwo ta hanyoyi da dama, wlhy wani abokin mijina suna hirar yanda a yanzu idan anzo tantance matasan da aka d'auka aikin Uniforms mafi yawan matasanmu Na arewacinmu suna d'auke da ciwon basu saniba, Dan ALLAH ki lalla6i mijinki kuje a abincika lafiyarku data y'ay'anku domin sanin halin da kuke ciki, ALLAH ya cigaba da bamu lafiya yakuma tsaremu baki d'aya, ciwone mai had'arin gaske da ake kamuwa dashi harta hanyar toilet. Karmuyi sakaci domin ALLAH😭🙏🏼_. *_Ya RABBI ka gafartama kakanninmu da iyayenmu baki d'aya, yayyenmu, k'annanenmu, y'ay'anmu, k'awayenmu, mazajenmu damu kanmu_*😭🙏🏼