Compiled by Umar Dalha Funtua. FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 BY 1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA 🐎HUGUMA GROUP🐎 Bissimillahi Rahamanin Rahim Allah ina rokon ka ka bani ikon gama wanan labarin lafiya da kuma nasara a cikin yin shi, Ya Allah zunun da zan kwasa a cikin sa kayafe min Ya Allah Alherin da ke cikin sa ka sadamu dashi ni da duk wani misullumi na duniya,,,, Ina mai rokon masu karatu da idan lokacin ibada yayi dan girman Allah kada a shagala a dinga aje karatu a aiwatar da duk abin alhari,,,,, nagode,,,,,, taku har kulun,,,,, ZEEE MAKAWA,,,,,, Sadaukar wa ga duk yan Family HARZAMI,,,,,,Tare da yan huguma group's Churching, sith Domenic Church ne da kowa yasan babbace church ne, daga cikin manyan churching da muke da su a kasar Nigeria, Church ce da akasari turawa ne ke zama father ko pastors din gurin, Wanda daga karshe har suke daukan yaran bakaken fata zuwa kasashen su don karo ilimin addinin kirstanci,,,, A kasarin mabiya wanan church din yan kabilar IBO, Kusan duk wani babban gari nada wanan irin church din inda yan kabilar IBO ke yawan zuwa bauta, Wana katon church din da ake taro yai a cikin garin kwantagora da da ke can cikin jahar Niger state, Da, alamar buki sukeyi a gurin yau kuma bukin mai girma ne da ganin hakan,,,,, Saboda yawan abin hawan da yau ya cika haraban churching, da kuma jama,a mabiya irin wanan churching da suka zo daga wurare daban daban acikin wqnan kasar,,, Sai kida kawai, ke tashi kamar kunnuwa za su fashe wa mutum saboda karan, kida, Matan church din sunyi anko har kusan kala uku kamar yadda mazan su, su kayi na su kallar anko din don kowa da tashi kalar shigar, Wani matashine dan kimanin shekara ashirin da takwas,, ke tsaye a harabar church din da alamar shima wurin taron ya zo,,, Dogo ne saurayin fari sol dashi, gashin kan shi sai sheke da walkiya sukeyi a cikin hasken rana, Sajen fuskan shi yadan kwanta mai kamar shi yayi wa kan sa, Kallo guda zakai mai kadau ka ko bafullatan,ce , shi, Saboda duk zubin shi na fulani ne, sak Tsaye yake, bakin wata bakar mota mai kirar landrove, jeep,,, Farar shadda ce, kal a jikin shi dinkin rigar ce ,mai gajeren hannu, a jikin shi,, Rigar an sa wasu manyan aninineya da akai ado dasu, a gaban rigar, Hannun shi daure da agogon company Rolex, irin na maza, dagani kasan na gold ne, agogon,, Sai wasu zubba da ya jera a yatsun hannun shi,, Kafar shi na saye da bakaken cover,shoes, sai sheki sukeyi, Sai, yar sarka da yasa a wuyar shi itama dai kallo guda zakai ma sarkan kagane cewa ta , gold ce, Kusan duk wanda ya wuce shi ta inda yake, tsaye , alokacin yana waya sai mai shi, yai mai hannu alamar gai suwa,, ta ban girma ko mutunci,, Hakan ne, ya nuna cewa wanan matashin sanane ne sosai a gurin wanan taron, da akeyi, Komawa yayi cikin church din ya zauna saidai kuma baifi minti ko biyar da zama ba wayar shi ta kara kara, kira ya shigo mai again,,, Mikewa yayi yana ma shugaban nin su alamar daukan umurni a gurin su, Baiwani dauki lokaci ba a waje wanan karon ya koma cikin church din ya zauna inda yatashi, da farko, Daidai lokacin anfara yawo da turen ansan donations kamar yadda suka saba idan suna taro, Yana jefa nashi envelope din ya mike batare da ko daga ido ba ya fara tafiya a daidai yar siririyar hanyar da aka tanada don bin masu fita da shige ciki,, Sukuma church din duk sun mike maza da mata suna wakar yabo ga almasifu,, Motar shi ya nufa direct, ya bude yai mata key yabar harabar church din Daidai lokacin wani tsoho iyamuri yafito daga cikin church din yana kokarin tsaida dan matashi mutumin da hannu,, Wanda shi a lokacin har ya fita daga cikin get din church din ko,,, Yana fita yai dan yi ajiyar zuciya, daidai da, lokacin da kuma,wayar shi ta dauki kara ke nan , A hankali yadauko yana diba mai kiranshi again, sai ya ga sunar mahaifin shi a jikin wayar barobaro, (MY DAD,) Barin kiran ya yi har ya katse tukun sanan ya kira mahaifin nashi , da kan shi,,, Duk a lokacin yana tukin mota,abinshi, a ran shi yasan cewa kiran shi mahaifin shi zaiyi ya dawo, Yadaga wayar yana mai fadin Alo, A can dayan bangaren aka ansa mai da Alon ba, Joseph where are u going now, Sai kuma tsohon yaci gaba da magana cikin harshen IBO, Yana cewa Baba ina da uzuri ne na fadama cewa yau nake son in koma portacourt, No, no no Joseph it can b, possible,,, I want us to pray for our successful, at home today night,, Yace cikin IBO har na yi inviting din pastor yuhana ko, Saida yadan diba agogon hannun shi tukun sannan yai yar tsaki cikin ran shi, Saboda baya son wanan addu,an da mahaifin shi ke sa ana masu agida, Don inda sabo ya saba ko da hakan,don tun suna yara ake wanan gaiyatar pastor a gidan su, Muryan tsohon ya katse mai tunanen shi inda yake cewa Joseph kaji abin da nace ma ko, Ya ansa mai da fadin Yes,, Dad,,, Yana jin ajiyan zuciyar da tsohon yayi a cikin wayar, Daidai lokacin da ya karya kwanan shiga uguwar kwanar kuka, ta inda zai sada shi da green,land, super market A nan ya dan tsaya wani shago yace a bashi katin MTN, Mai katin ya ce na ,nawa za a dauko mai sai yace na dubu goma, ai sai mai kati yaja yai tsaye, Don shi a zaton shi, gatse ake mai, Shiko a lokacin hankalin shi na can yana bidan wani takarda da yake son yaba mai shi, Yana dago kai yaga ko mai shago ya kawo mai katin sai yagan shi tsaye gaban shi, Hannu ya mika don yakarba sai mai shagon katin ya ce mai a nadauka bakar magana kai min, sir Cikin mamaki yake kallon mai katin shiko ya koma da sauri don dauko katin, Saidai mai shago ya tarar da katin bai kai na dubu goma ba don haka ya tsaya yi mai bayanin baikai ba , Hannu ya mika yakarbi wanda yasa mu yana mai mika mai kudin da yakirgo dubu goma, Cikin mamaki mai shago yace ai na dubu bakwai kawai aka samu maigida Cikin hausar shi kamar ba haihuwar IBO ba yace, kabar shi kawai daidai lokacin da yata da motar shi yabar gurin, Mai shagon katin yai tsaye sororo ya bi shi da kallon ikon Allah,,, It's been a long day without you my friend and,i will tell you all about it when i see you again ,we have come a long way from where we began,oh i will tell all about it when i see you again, (Wiz_Khalifa feat charlie puth) SEE YOU AGAIN, Baka jin komai a cikin motar sai wanan wakar ke tashi yana kokarin loading kudin da ya saya awayar shi, yana maming din wakan a hankali,,, Phase 2 ya karkata motar shi zuwa, hanyar tudun wanda don yai saurin kai shi uguwar, phase 2,, din Daidai, roundabout din da ya mike zuwa,Kwangwara, da Kan Wuri, Ta, window motar ya ga ana mai hannu alamar ya tsaya, dan murmushi yayi dan ganin wanda ke kokarin tsaida shi a lokacin,,,,, Wuri ya samu a gefen hanya, ya parker motar shi daidai lokacin da wanda ya tsaida shi ya iso gurin,, Hannu suka mikawa junar su alamar gaisuwa a tsakanin su, Cikin nuna jin dadi daganin junar su yasa suka rike junar su, suna ta dariya, Kafin minti biyu sai ga gurin da suka tsaya yafara cika, Duk wanda ya gansu cikin farin ciki yake tsayawa ya basu hannu, Mutane da ke wuce wa sai kallon su sukeyi cikin mamaki, Komay ke faruwa haka aka tsaya a gefen hanya,,,,,, ZEEE MAKAWA, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣ BY ZAINAB IDRIS MAKAWA 🐎HUGUMA GROUP🐎 Fatan alheri ga dukkan wayanda suka nuna min kaunar su da kuma kulawa, Sai misalin karfe shidda da wani abu yadawo gida daidai lokacin da abokan shi ke shirin alwalal sallah magrib ,, Tun fitar shi yana can phases 2 tare da abokan shi Friendship din su ya dauko asaline tun a makarantar primary, daga nan kuma suka jona secondary, Tun a lokaci baida wasu abokai sai yaran hausawa Duk irin fadar da mahaifin shi da yan uwan shi ke yi mai bai sa ya daina bin diyan hausawa ba, Kamar yadda akasan diyan IBO da rashin son dan bahaushe shi nashi halin na daban ne, Don har abincin su yake ci ,idan yaje gidajen su, ziyara lokacin yana karami, Bayan rasuwar mahaifiyar shi baban shi yaga cewa duk akidar shi kusan na hausawa ne yasa shi dauke shi zuwa kasan su don ya karasa karatun shi a can, Yana gamawa sai kuma akatura shi, kasar Malaysia yin karatu can, Acan Allah ya hada shi da dan wani millioner, dan yaren su na IBO Amma shi bai,damu da karatun da sukaje yi ba, Sai Allah yasa shi da ya maida hankali yana hadawa har da na Emzon yayi mai su test da sauran aiyuka, Exam ne kawai, Emzon kezama yayi a haka har Allah ya taimake shi suka kare karatun su, Bayan dawo wan su karatune Emzon ya jona Joseph, a business din harkan man petrol Daga haka Allah ya taimake shi ya cigaba tun suna yi da kudin Emzon har suka daina hada kudi a tsakanin su,, Wasa,wasa Joseph ya fara na shi harkan sai gashi ya canza wa uban shi sana,a daga saida manja, yakoma harkan petroleum, shima,,,,,, A kofan gidan su ya iske baban shi zaune a saman wani benci, da wasu yan dattijawa kamar shi Kwalaben giya ne suka tara birjik agaban su, sai shewa suke yi suna ta hayaniyar hiran irin bidirin dazun da akayi,,, Yadan dade zaune cikin motar shi kafin ya fito ya fitowa sai yai kokarin bin ta kofar baya don ya shige cikin gida, Muryan Mr Emanuel yaji cikin yar buguwa yana kiran shi yazo su gaisa da abokan shi,, Bsdon yaso ba ya karaso har inda suke zaune, Kwalban giya yake kokarin mika ma dan nashi yana wani irin dariya sama sama, Kai kawai Joseph ya kada mai alamar a,a ya taka tabaya yadan juya zuwa cikin gida, Yana shiga wanka ya wuce yi direct bayan fitone ya iske wayar shi na ringing, KB aka rubuta barobaro a cikin harshen hausa yace KB ya,ya dai,? KB ya ce mai yaga jibrin din da yake bida yadawo gari shiyasa ya kira shi don yafada, mai Yace ka gane ne KB yanzu kabani a wa biyu pls, zan zo in samay ka muje gidan su, Eneka sister shi ce tafado Dakin tana cewa brother muna jiran ka a,palour pa, Saida yadan kara kamar minti goma yafito cikin wasu yan kananin kaya, Yasamay duk a rusunne pastor yana tsaye sai addu,a yake zabgawa suko suna ta fadin Amen, Amen, Bin sahun su yayi ya jona su a haka akai ta masu wana addu,an har zuwa wani lokaci, Baban shi dama a buge yake tatil da giya tun a nan ya tuntsire ya fara nasari, Joseph ya ciro kudi tare da dafa ma pastor baya har zuwa gurin motar shi, ya mika mai kudin yana nuna godiyan su da wanan ziyarar da pastorn yai masu,,, Daga nan baikoma ciki ba, ya wuce zuwa inda KB, ke jiran shi su tafi, Gidan su jibrin Bala suka tafi cikin daren nan, Jibrin na cikin gida akace wai ana mai sallama, Bai wani bata lokaci ba yafito , yayi mamaki kwarai ganin Joseph yasa shi yin wani dan ihu, har saida yajawo hakalin mutane,masu wucewa, gare su, Yayi farin cik kwarai da,ganin Joseph yace Yusuf Joseph ke nan duk sai suka dariya a lokaci guda saboda, tuna wa da wani zamanin da yawuce a baya, Inda Joseph ke cewa shima sunan shi Yusuf Joseph, ne, kama yadda Kabiru lawal Jibrin Bala,sai Musa Aliyu, Shima Joseph sai ya cire Joseph Emanuel ,, Yace ya koma Yusuf Joseph, Dariya yayi yadankai wa jibrin din dan duka ga kafadar shi cikin dariya, Suka kara lalewa, da junar su, nan fahira ya barke a tsakanin su na yau she rabo, Sun dauki wani dan lokaci sanan sukabar uguwar yamman inda gidan su jibrin bala din yake,, Kafin su rabu Joseph ya debo kudi masu yawa ya mika wa jibrin din yana mai bashi hakkuri, Kan cewa bai san cewa zai kwana ba don bukin yazo na nada sabbin shugaban nin church din su da akayi, kuma duk ya kashe kudin shi ga jama,a Tun da ya aje KB a uguwar tukura, yasa kai zuwa gida ziciyar shi fam da tunanen halin yadda ya ga abokan nashi ciki, Duk da goma na dare ya wuce har da rabi hakan bai hana shi cin ma yan uwan shi zaune suna jiran shi ba, Ya bude falon kusan lokaci guda bakin su ke cewa brother welcome, Ya ansa masu da ce how you na dey,? Saida yadan shiga daga ciki tukun sannan yafito cikin wasu yan kananin kayan barci, Sai a lokacin ya tuna cewa bai co wani abinci ba don haka inda suke cin abinci ya wuce sakwara da miyar ego yaji egushi da naman shano, Ya wanke hannuwar shi ya fara ci, sai da ya gama cin abincin sanan ya isa, inda yan uwan shi suke zaune yake tambayar su inda baban su yake, Da hannu suka nuna mai hanyar kofar dakin shi, Anan suka fara mai korafi kowa da abinda yake so amai da ga cikin su,,, Wa yanda zaiba kudi yaba su, wa yanda kuma zai, sayo wa abu yai masu alkawari, Tunda safe yai asubanci yabar gari yadauki hanyar lagos, saidai zuciyar shi fam yake da tunanen yadda ya yaga abokan shi suka koma cikin dan lokaci guda,,, Bayan tafiyan Joseph abokan shi suka dinga rumors a gari cewa Joseph yazo wasu su ce yadawo, Kafin wani lokaci sai maganganu ya karade gari wasu nacewa aiki yasamu mai tsoka, Wasu nace harkan business din zamani yakeyi watau, dai smuggling, wasu kuma suka ce ai dan shan jini ne, Inba haka ba ya zaiyi kudi haka cikin dan lokaci guda, kamar yafi su bida, KB ne a saman babur din shi, yana tafiya zuwa gidan wani dan uwan su don ya kai sako, Hadewa sukayi da jibrin a daidai junction, anan suka dan tsaya don su gaisa, A haka suka sako hiran Joseph cikin zancen su, inda suke yaba alherin da yazo yai masu, KB yace wai ko kasan cewa mutane da daukar wa kan su wahala da nauyi wai har sun fassara dukiyar Joseph da wata, ma,ana,,, Cikin mamaki jibrin yace kai mutumina bari zancen nan pa, Yace wallahi man ni ma su jamil suka tare ni hanya suke ce min wai ko da gaske ne zancen da sukaji game da Joseph ance wai yayi fitacen kudi, Jibrin ya kada kanshi yace kai mutum mutum abin tsoro ne wlh, Yanzun nan har sun fassara wanan guy din dawatq ma,ana ko, Allah ya kyauta kawai suka iya cewa suka dan kara taba hira sukabar gurin cikin alkawarin kara haduwa nan gaba, Daidai wanan lokacin Joseph yana zaune a cikin kayattacen falon shi da garin lagos zaune yake cikin shigar kananin kaya, Kallo guda zakai mai ko ba,a fada maka ba zakasan cewa kaya ne, masu tsada a jikin shi, TV yake kallo a zahiri saidai gaskiya ba wai abinda ke faruwa a cikin TV yake kallo ba, Don dai zuciyar shi na can tana tunanen abokan shi na kurciya da yagani cikin halin taimako,, A hankali ya furzar da yar iska daga bakin shi yana dan bugun hannun shi a hankali, Jinkarar bude kofar da akayi a lokacin ya dan waiga don ganin wanda ya shigo cikin falon a lokacin, Inok ne ya shigo wani abokin shi ne da suke yawan mu,amula indan yana Lagos da shi, Inok yazo inda yake suka yar lalai hannu cikin nuna kulawa, Inok yana kaiwa zaune yace wa Joseph kai aboki nai muna sabon kamu fa, Duk da nasan cewa kaiba dan wanan harkan bane , nasan cewa wanan karon zaka kamu sosai indan har kaga cik din nan,,, Kwantar da bayan shi yayi a saman kujera yadan waigo inda Inok ke zaune yana murmushi ya ce nagode da gudun mawarka amma kasani cewa ni wanan harkan bata a gabana yanzun haka, Indadai wani business ne kasamo muna danafi kowa farin ciki da kai yau, Baki bude Inok ke kallon Joseph yana mamakin irin halinshi na ko in kula ga mata, Gashi dai yaro matashi mai jini ajika aman ba ruwan shi da harkan mata,, Sai cewa yayi wai kai joe wani irin guy ne kodai matane baka so sai maza, Cikin mamaki Joseph ya kalleshi alamar mamaki karara a fuskan shi yace God forbid bad things,,,,, Me, Joseph doing such bad habit in my life never,,,, Daga haka yamike tsaye ya haye sama abinshi ya ma kulle kofar dakin shi yabar Inok zaune a falon Ido kawai Inok ya bishi dashi har zuwa lokacin da Joseph yabugo kofar dakin da karfi Inok ya mike tsaye yana mai watsar da hannuwar shi alamar haka take gare shi, Sai da Joseph ya tabbatar da cewa Inok yabar gidan sannan ya fito ya dauki makullin motar shi yabar gidan cikin kunar rai, Direct inda suke shan whisky ya nufa can ya zauna yadan sha kadan sanan yabar gurin zuwa gidan wani kawun shi da yake son ziyara da dadewa, A can gidan yakai dare tare da uncle Sam, inda suka dan taba hira gamay da halin da family su ke ciki, Kafin atafi saida yaiwa babban dan uncle sam , alkawrin samun aiki, Sai bayan yadawo kamar da kwana uku ne yakira nobar wayan jibrin da yabashi ranan da suka hadu ,,, Sun kai wani dan lokaci suna hira cikin mutunci inda suke ta hiran classmates din su,, da kuma irin gidajen da suke zuwa idan antashi makaranta, Sunyi dariya sosai idan sun tuna da wani abu da sukayi ada suna yara,,,,,,, A haka sukyi ban kwana da junar su har zuwa wani lokaci,,,,,,,,, Kwance yake yana barci a saman tangamay may gadon shi, Karar wayace ta katse mai barcin dayakeyi , a hankali ya diba kowaye yakirashi cikin dare haja, Monday yagani rubuce, acikin muryan barci ya dauki wayan ya kara a nunen shi yace, Hello, a bangaren Monday ya ansa da cewa hello sir, Anan Monday ke sheda mai cewa wai motar man su guda da aki loading zuwa westnorth ta samu matsala a hanya har mai ya tsiyaye, Awani dan kauye kuma sunyi iya kokarin su su tasarya abin ya gagara shiyasa ya bgo mai wayar,, Mikewa yayi zaune daga kwanciyar da yayi batare da yaba monday ansa ba ya kashe, wayar,shi, Wurin window dakin shi yanufa tsaye yake yana kallon hasken fitilun da yadan haska duhun dare, kamar yadda taurari suke haska sama, A fill ya furta Monday, I will delling with u, soon, gurin fridge ya wuce yadauko ruban ruwan sanyi ya kwakwade shi dukka, lokaci guda ya cillar da robon kasa,,,, A ranan barci rabi da rabi yayi don zuciyar shi na kuna ga irin rainin hankalin dasu Monday ke yi mashi, Don kashi na uku kenan suna mai wanan hasarar da kuma wawaso, Tunda safe ya shirya tafiya zuwa arewa batare da sanin kowa ba, Sai da yai nisa yai wa KB waya, yana msi tambayar shi idan har bai komai yana son ya raka shi wani uguwa, A suleja suka hadu, suka kama hanyar zuwa inda minday yace sun samu matsala, Har zuwa adamawa babu tanker motar dasuka hadu da ita a saman hanya, da zasu dawo kuma suka kara bi ta wani sabon hanya da akai masu kwatance Still a nan ma basuga komai ba, sai mota guda suka fani kuma ba ta company su bace , Kiran monday yayi yace ya fada mai daidai inda motar tasamu matsala gashi a cikin North, Cikin rudani Monday yace what, You mean you are in North now yace mai of,course, Jin yadda monday ke in,inniya yasa shi kashe wayar shi,,,,,,,,, ZEEEEE MAKAWA,,,,,,,,,,,,,,, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJ 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣ BY ZAINAB IDRIS MAKAWA 🐎HUGUMA GROUP🐎 Assalamu Alaikum yan uwa dan Allah kuyi hakuri don ina sane da sunan da yakamata in sa wa , wanan novel din sai dai a gaskiya ina ganin kamar akwai wace ta riga tayi novel da wanan sunan, ( FUREN KAN JUJI) Hakan yasa na can za wa nawa suna namaida shi FUREN JUJI dafatan zakuyi maneji dashi hakana,,, nagode,,,,,,,, Sai musalin shadayan dare suka isa cikin garin kwantagora, Gidan su KB ya wuce direct don ya sauke shi, tare da tsarabar da sukayo ma yan gidan su KB din, Tsarabar doya ce da manja,don saida buth ya cika fam, Acikin daren ya wuce zuwa gidan su dake can uguwar sabon gari, Duk da dare yayi amma yasamu yan gidan su sun dawo daga church suna kokarin cin abinci, Cikin murna da farin ciki suke tariyan shi, shiko ya na dan buga masu kafada ahankali, Inda mahaifin shi yake zaune saman dogon kujerar dake falon gidan nasu da gashi sai yar singilati da gajeren wando, Sai abin fitar da ke a hannunshi yanadan fifitawa a hankali, Daidai satin kafan uban yadan duka inda uban yadan dafa mai kai ya na cewa you are welcome, ba,,,, Joseph Why d, you like to travel in d night ? Sai kuma yaci gaba da fadin cikin har shen IBO, Dan Allah ka daina tafiyan dare saboda hanya da bai da kyau so sai, Murmushi kawai Joseph yayi yana cewa ba abin da zai faru by god grace,,, Kayan shi yasa aka shogo dasu inda uban ya kalli kayan yace Dat means u are going to stay long, ba,,, Yace cikin IBO yes dad akwai abinda zamuyi ni da abokaina a nan garin, wani irin ihu yayi kamar yadda IBO kanyi idan sunji abinda ya taba masu zuciya, yace hyyy Cineke God Woooo, Joseph Why ,u no dey, hear word, Nafada ma karabu da yaran hausan nan but still kaki, Kayi hankali kada su jefa ka a cikin wahala watara na, Kokarin shiga ciki yakeyi alokacin yace, nothing will happen Dad, Daga haka yai shigewar shi ciki ruwa ya watsawa jikin shi, sanan yafito , Saman kujerar dake falon ya, zauna gurin zaman mutum daya, Duk da agajiye yake sai kuma yunwar da yake ji, tuwon teba da miyar egusi, aka aje mai a gaban shi,,,,,,,,, Sai musalin shadayan rana yafito cikin shigar suit farare sol sai yar kwalar shirt din cikine kawai pink colour, Yar jakar da yashigo da ita ya bude yadauko rapan yan dari bibiyu dana dubu guda guda yasa a cikin aljihun shi, Wayan shi ya dauka yana latsa nobar KB yace Hello KB kana gida ne yace mai eh ai na kira wayar ka yana akashe, Yace ko zan samu kunu da kosai a gidan ku pls, Saida KB yai yar dariya sannan yace mai baran diba ko akwai, shi, a ciki don na shanye nawako, Daga haka suka kashe wayar su, inda KB yashiga ciki gurin mahaifiyar shi yana tambayar ta ko akwai kunu, Cikin mamaki umma ke tambayar Kabiru may zaiyi da kuna bayan wanda akasa mai, Yace mata Joseph ne ya bugo min waya yana son kunu da kosai, Ikon Allah tace shi,wanan yaron har yanzu yana cin irin abincin mu, Ba bata lokaci ummah ta hasa wutar dama kunu inda taba kabirun kudi yaje ko za,a samu kosai, Saidai sunyi kicibis da Joseph din a kofar gida yana Parker motar shi, Tare sukaje gurin sayen kosai ba,a samu ba don haka suka dawo gida, Ummah tasan halin Joseph tun suna yara, kuli,kulin suga ta aje mai tare da sugari , Bakaramin murna yayi ba don yace rabon shi da kuli,kuli tun a wancan lokacin, Abin yaba ummah mamaki gani andawo mata da jug bakomai dik an shaye, kunun, Koda ta bude kwanon kulikuli sai kudi tagani aciki yan dubu dubu har guda goma, Cikin sauri ta,ce amayar mai da kudin shi, badon yabata wani abu ba tai mai shi, Koda yaron yaje saiga Joseph ya shigo rike da kudin a hannun shi, Salama yayi kamar musulumi har ummah ta amsa mai sai da ta daga kai sai taga ashe Joseph, ne, Tai saurin yin astangafullah a cikin zuciyar, ta, nan da na ta hada fuskan ta, ta tare shi da cewa haba Yusif don nadama ma kunu zaka bani kudi saboda may zakai mun haka, Saida yadan sha fa kan shi tukun sannan yqi yar murmushi Yace haba Ummah aiko baki bani kunu ba zan baki wanan kudin, Nabakine don neman albarka a wurin ku ba wai don abinda kin min ba,,,, Shiru Ummah tayi saboda maganar ta kashe ma ta jiki so sai, Sai bude baki tayi tana mai cewa Allah yai ma albarka Yusuf Allah ya karkato ka kagane hanyar gaskiya, Murmushi kawai yayi batare da yace mata komai ba, Hannu yasa a aljihu ya ciro yan dari bibiyu ya ba sauran mutanen gidan, Har zai fita saiga baban su kabiru ya shigo, gidan da alamar kasuwa yafito don kayan cefane ya sayo a cikin leda,,, Shima sun gaisa yabashi nashi Alherin, daga nan suka fita, A wanan ranan sun sha yawo da KB don duk gida jen da yake zuwa lokacin yana karami saida KB ya kai shi yai masu alheri, A karshe suka je gidan wata kawar maman shi da ta mutu, Matar a,na ce da ita salama, irin matan nan ne masu sana,ar Manja a cikin gida Hakan yasa tasaba da maman su Joseph din, sosai har yakai zata ita daukan man ja ko da jarka nawa take so, Sai sabo mai karfi ya shiga tsakanin su sosai, Har zuwa lokacin da maman su Joseph tasamu accident a hanyar ta na dawo wa daga kasar su bukin chrismatic, Har bayan rasuwan maman sukan je wurin Salama mai manja, Saida yabar kasar ne wanan alakar ta mutu tsakanin Salme da su, Yau kwatsam saiga shi yace KB ya raka shi gurinta, A bayan Neper gidan Salame yake, Gidan yana nan kusan yadda yasan shi bai wani can za ba, Sunyi sallama akace masu wasuke nema sai KB yace ace gurin salama suka zo, Mamaki salama tayi don jin ance wasu samari biyu ne da wata katuwar mota, Don ita a iya saninta bata da wani mai irin wanan motar, Balle yazo gurinta, tadauko tsohon hijab dinta ta saka akan ta cikin dan sarsarfa ta isa kofar gidan, Salama nan kamar yadda yasan ta saidai tadan kara manyata sosai fiye da ,dai, Yana mai, murmushi lokacin da ya hangota ita ko ,sai kallon mamaki take masu don har KB din bata gane ba, Tana isowa inda suke duk suka dan duka suna mata ina wuni, cikin ladabi, Ta, amsa masu tana cewa daga ina fa samari, kodai wani kuke bida, ne, Dariya suka dan yi KB ne yace mama Salama baki gane mu bane har da ni, Tadan kada kai tace gaskiya kan ban gane kuba, Cikin hausar shi da ke nuna cewa ba pure bace sosai yace, Mama kin manta da Dan ki yaron mama Ebele, Yusuf Joseph,,, Cikin mamaki ta kama bakin ta tana cewa ,a,a,a dan gidan mama Ebele mai man ja kai ne, Allah sarki ina ka shigr haka duk wanan dadewan haka, Nazata ai munyi bye da kai kenan kabar wanan garin Don nasha tambaya ana ce min kana kasar waje, kaje karo ilimi, can,,, Tace barin samo maku abin zama ko, har suna hada baki gurin cewa a,a barshi kawai mama, To barin kawo maku ruwan sha ko shimadai sukace tabar shi , Sunzo kawai ne su gaishe ta, Sai takama sa masu albarka tana godiya ga karamcin da sukai mata na tunawa da ita bayan wani loakaci, Kudi ya mikawa KB yace yabata, amma tayi hakkuri zai dawo badadewa ba ,,, Saida kudin yabata tsoro don a gsskiya ta dade rabontq da kudi masu yawa hakan ga, Taitayi mai addu,a tana sa mai albarka da fatan gamawa da duniya lafiya, Nan yaga wasu yan tsofi maza guda biyu saman wani tabarma ya basu, dubu guda guda, Har ya bace sunayi mai addu,a da fatan alheri suna kuma tambayar kowaye, Salama ta fada madu cewa dan waje Ema mai manjane tsohuwar kasuwa, Tsohon guda yace Allahu akabar ashe FUREN KAN JUJI ne shi, gashi yaron kirki amma ba jinsin kwarai,. Dan gidan Ema kan ai babu batun musulunta gare shi sam, Gudun tsohon mai dan magana da sauri sauri yace kasan abin Allah yawai gare, ai, In har mutum bai mutuba ba,a gama halittasa ba ai,,,,,, Su kace wanan gaskiyane, Allah ya taro shi ya gane hanyar gaskiya,,,,,,, Town holl akayi taron na matasa, tsofin daliban SANI BELLO,nursery _ primary & Secondary school,,, Inda taron yabada ma,ana sosai ga cigaban da matasa keson kasar su ta samu nan gaba,,, Bayan wanan taron ne akai ta hotuna tare da exchange din nobar waya a tsakani, Koda suka bar gurin taron har duhu yafara don haka su KB da sauran friends suka nufi massallaci, daidai lokacin da suke alwala, ne shi kuma, Motar shi ya shiga yatayar duk kusan wanda ke gurin sai da yatau saya mai azuciya ta kasan cewar Joseph Christian, Gadai mutun har mutum amma babu alkibilar kwarai a rayuwa, Shiko yana barin gurin Church ya nufa don ya samu evening preys,, Mr Emanuel yayi farin cikin ganin motar Joseph a harabar Church din a wanan lokacin da bai tsamani ganin dan nashi ba, Sunkai kusan goma nadare sanan suka dawo gida, inda nan suka zube a harabar gidan aka kama yan shaye shaye, su nan,,, Har safe Joseph na abuge don ba karamin giya baban shi ya dirka mai ba daren jiya, Don kawai jin dadin kasan cewar su tare cikin wanan lokacin,,,,, Sanmako su KB sukayi zuwa gidan su Joseph saboda sunyi alkawarin yin sanmako zuwa wani kauye can guraren daki takwas,,,, A irin yanayin da suka samay shi yasa jikin su yan sanyi Don sam basu zaci cewa yana sha ba, don basu san shi da hakan ba, Tafiyar tasu dole suka fasa suka barshi nan ya zuba shirmay shi suka tafi abinsu,, Sai bayan karfe biyu ya farka a lokacin ya walwake sarai, wanka yashiga, Yana fitowa ya zauna cin abinci , saida ya koshi saboda irin yanayin da yake jin cikin shi kamar duk an kwakware mai kayan ciki,,,, Sai bayan ya koshi ne, ya tuna da zancen tafiyan su, cikin wani irin zabura yace, Jesus, Christ,,, Saida kowa ya kallo shi don jin abin da ya ambata,,, Wayan shi ya lalaba cikin sauri,ya diba yaga ko da , KB yakirashi zancen tafitan su, Gañin babu called yasa shi saurin mikewa nan yabar abincin da yafara ci yanufi hanyar fita da sauri da dan makullin motar shi a hannu, A,majalusar su ya samay su sun cika kamar kullun, Can nesa kadan ya aje motar shi yafito ya kulle ko ina Hannu ya mika masu don su gaisa da kowa , amma fafir Jibrin yaki mika mai, Yunus wani bayerabe da ke cikin su yace wa jibrin ana baka hannu fa,, Jibrin yace ai na gani bazan karba bane kawai, duk wurin saida kowa yai mamakin jin kalaman jibrin din, Shi kanshi Joseph din abin yadamay shi amna sai kawai yabasar da zan cen yai yar murmushi kawai, Azuciyar shi yace indan kasan mutum to kada katambayi halinshi koda bayan shekara nawa ne,halin na nan, Don haka yasan akwai abinda yai wa jibrin ke nan, amma saidai shi a iya sanin sa bai mai komai ba, Saida , karfe shidda yayi jibri yace kai joe muje ka kaini gida, Babu musu joe din kamar yadda suke kiran shi idan sun so, shi ne guy name din shi,,, Tare da KB suka fita su uku, sundan fara tafiya ke nan Jibrin yace Kai joe samu wuri ka parker zamuyi magana ne, Ba musu ya parker motar shi inda Jibrin din ya fara magana cikin fushi kamar fada, Joseph yaushe ka fara shan giya, don dai iya sani na dakai baka irin wanan dabi,ar sam, Duk da ku a gare ku ba abin kunya bane, to kasani cewa mu kan agurin mu wani babban al,amarine, Muddin gari akasan kana wanan dabiar gaskiya dole muma mu rabu dakai don gudun zargi a gare mu, Saboda jama,a zasu iya fassaramu dakai duk abu guda mukeyi, Kamar yadda kasan mutanen ka na kyamar zaman mu dakai muma hakana namu mutanen suna ganin mu da rashin sanin ciwon kai, Abune kawai idan Allah ya hada, babu mai iya hanawa, Tunda Jibrin yafara magana Joseph yana rike da sitiyarin motar shi amma gaskiya bai tsamani maganar da Jibrin ke ma fushi ba ke nan, KB ne yakarbe da cewa duk addinan mu ba wanda ya yarda da shangiya balle har mu dauke shi kamar abin ado, Jibrin yace wai ma yaushe ka fara shan giya ne man Hannu yadaga masu yace is over pls, Yai ma motar shi giya suka bar gurin batare da wani ya kara magana ba, Saidai gabadayan su , sun sancewa shikenan kamar yadda yace is over din yadaina kenan har abada,,,,, ZEEEE. MAKAWA,,,,,,,,, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣ BY ZAINAB IDRIS MAKAWA 🐎HUGUMA GROUP🐎 Mama Farida & Maman Walid Kuna raina ko yaushe fatan alheri gare ko kamar yadda kuke min akullun,,,, Maryam , maryam, wai may kikeyi a ciki ne haka, ? Ki diba time ki gani yanzu kusan karfe biyar ake bida fa, Wallahi anty Assalam ne yaki tsaya in shafa mashi mai waishi saidai ya shafa da kan shi, Anty Dije wace ke kitchen tana kokari dora sanwar marance , Itace ta fado dakin a hasale tana kokarin bugun Assalam din wanda ke gefe guda tsaye shi adole bai son anty ta shafa mai manshafi, Cikin sauri Maryam ta tare, da hannun ta inda anty tasamu hannun maryam din Maryam na gane cewa har dake cikin shagwaba Assalam wallahi, Aiku da malam ne idan har kun tafi kun iske an tare get, A gagauce Maryam ta shirya yaran cikin kayan islamiyar su, ta dauko yar jakarta wace yan mata kewa lakani da wankar gefe, taraya a gefen ta,,,,, Cikin sauri ta riko hannu Issalam wace ke tsaye tun dazu cikin shirinta tana jiran su tafi, Murya ta daga daga inda take tana fafin Anty mun tafi sai mundawo,,,,, Agajiye suka shigo garin na kwantagora daga kauyen da suka tafi cigiyar Dawaki da Rakumai wanda suke son suyi wasan Dabah dashi Direct gida kowan su yatafi, shiko Joseph yana shiga gidan su yatar da ba kowa agidan duk sun tafi gurin bidan kudi, Yar tsuki yaja azuciya shi yace bidan kudi tun bamuzo duniya ba kulun ana shago ba hutu, Wanka yayi don yadan ji sanyi a ranshi, bayan ya fito wanka ne yadawo falo ko zai samu wani dan abu yaci,,,, Saboda hura su KB suka sha a kauyen shi kuma bai iyan shan hura yan zu, Don koda da yake yaro yana sha bai bashi lafiya, Don,haka wurin fridge ya nufa ko zai samu dan abin da yaci a ciki, Giya yagani kala,kala ga sunan, tab acikin fridge din, Iya dibawan shi bai ga komai dazai danci ba sai giya kawai yagani, Har ya mika hannu yadauko kwalbar wani whisky da yake yawan sha, Muryan jibrin yaji yana cewa both religions din mu ba wanda ya yarda da shan giya, Giya tana zubar da darajan mutum, Da sauri ya dafarar da kwalbar inda akasane ba cikin fridge ba da ta fashe ko,, Ya mai da marfin fridge din da karfi ya rufe , yajuya da sauri yabar gidan, Har yafita sai ya tuna da cewa bai dauko makullin motar shi ba, da handset din shi don haka sai ya koma ciki, Warin giya yaji yau falon nasu nayi a sakamakon bude fridge din dayayi sai kawai yaji warin na hawa mai kai,,, Maimakon ya shiga mota sai yafita get din su ya taka da kafa,don yatari mai achaba ya hau, A hankali yake tafiya har ya kusa shan yar kwanar gidan su sai yaga andanyi taro a gurin Kamar ance mai yatafi har zai wuce sai kuma ya isa gurin, Wata matace yagani tana ta rusa kuka ga wasu samari suna ta kokarin yin bico a wani fili, Matar na fadin wallahi bamu sayar wa kowa da filin mu, ba kudine kawai bamu dashi shiyasa bamu gina komai a ciki ba, Ya dan tsaye daga baya tana kallon ikon Allah, inda yawancin mutane gurin ke cewa ai fillin na matan ne ita da yatan ta, Sun gaji fillin nr gurin mijin ta da yarasu, lokacin yaranta suna kanani bata da halin gina filin Yanzu ko yaranta sundan girma shine tazo dasu don sugyara filin su dan samu wurin zama koda bukkah ne su dan haka saboda gidan haya yana mata wuyan biya, Sai gashi sun fara aiki kenan wani yazo yace ai yasayi filin a gurin kanin mijinta, Kuma har ya biya kudi dadewa, don haka subashi wurin shi, Matar nata kurma ihu tana cewa ta shiga uku babu inda zata ga yara gashi basu da kudin biyan haya Joseph na tsaye yana jin yadda matar ke gumza kuka duk wanda yazo yaji ba,asi sai dai ya ce Allah ya ktau mai shi ya wuce abin shi, Duk yunwar da yake ji sai yanemay ta yarasa , Takawa yayi har inda mutumin da ke ciwa matar mutunci yake, yai mai sallama yana mai mika mai hannu, don su gaisai, Bayan sun gaisa ne yake tambayar mutumin ya maganar take ne, Da kamar bazai bashi ansa ba saidai yadda yaga Joseph din is serious sai ke ce mai Yar rainin wayo ce sun saida filin su dadewa shine yanzu tazo wai ita zata gyara wa yan marayun ta, Wazata nuna wa marayu nida tunda nataso banda kowa balle, Wani irin kallo Joseph yai wa mutumin don jin maganar rashin imanin da yayi, Hannun shi nazube cikin aljihun,farar wandon shi dayasa ya juya dakyau yana facing din mutumin, Ya yanzu may kake so kai tunda kaji mutane sun sheda cewa filinta ne ita da yaranta, Mutumi yace kadaina cewa filin ta fa malam kace filina, Daidai loacin matar cikin kunar rai tace karya kakeyi muna fukin Allah, Joseph ya waiga gurinta cikin hausar shi ya ce kai haba kibi a hankali mana mama, Ya juyo gurin mutmin yace to nawa ne kai ka sayi filin malam,? Mutumin yadan yi dumm can kuma sai yace wai dubu ashirin da biyar, Wani mutum dake gefe yace kai malam Bawa, dubu goma sha biyar fa aka sayar ma, Joseph yadaga masu hannu yace Ok yanzu fadi muji nawa zaka sayar mata ita da yaran ta, Nan da nan gurin yai tsit ana sauraren su, Malam Bawa yadan yi tunane can yace in an saye hamsin na sayar in ba asaya ba shikenan ni inada abin yi, Matar takara sa kururuwa tana cewa Allah ya isar mata ita da yaranta akan mutumin da kuma kanin mijinta, Nan da nan gurin ya shiga hayaniya kowa na fadin albarkacin bakin shi, Joseph yakalli mutumin yace mai in bazaka damu ba zan baka dubu talatin yanzu gobe ka turo in karasa maka sauran don ban fito da kudi ba, Ai ba laifi inji malam Bawa nan da nan mutane suka kama cewa wai kada akara mai ko kwabo abarshi hakana macuci, kawai, Gurin matar Joseph ya karasa yace mata mama nawa kudin hanyan ku tace mai dubu daya da dari biyar ne wata uku, Dubu biyar yabata yace taje tabiya haya saura,tasayi abinci suci Zuwa gobe zai nemay ta, zai san yadda za,ayi, Yazo zai wuce yaji wani mutun yanawa wasu mutane bayanin cewa Saida Dan kahirin can ya taimaka mata yaba malam bawa kudin shi, Duk da rashi ya baci murmushi kawai yayi ya tqre mai achaba da hannu ya hau yana cewa kaini Green Land,,, Ya samu majalissar su KB ta cika anata hira saman wani tabar ma wasu kuma zaune a saman wani benci, Gefe guda ya samu a saman tabar man yadan kwanta rigingine fuskan shi na kallin titi yana kallon masu wucewa, In akwai abinda maryam taki jini a rayuwar ta shine idan zasu wuce ta iske wanan majalissar ta cika, Duk da bata kallon gefen su amma tana tsarguwa don ji takeyi kamar duk ita suke kallo, Tunda ta tun karo gurin taga sun cika duk sai taji ba dadi aranta don haka sai ta dan kara sauri tana rike da hannun Issalam, Shiko Assalam na bayan su yana shuka tsiya wai bazai tafi ba don haka suka dan yi gaba suka bat shi, Saida yakawo dai tsakiyar inda majalissar matasan yake ya yanke jiki yafadi wurin kalle kallen shi, Aiko ya yanka wani irin ihu kamar wanda aka zare wa rai, Duk wanda ke gurin saida ya waigo inda yake kwance cikin kasa yana faman kurma ihu, Wasu daga cikin yan majalisar suna ce mai tashi ma na wani kuma na ce mai dan nema wurin shegen kallo har ka fadi, Dole Maryam tadawo baya ranta duk a bace, Joseph dake kwance yana kallon tun gilmawan su maryam har zuwa faduwan yaron wanda yai tuntube ya fafi kasa, Yataso daga inda yake kwance,yazo inda yaron yake yanata tsala ihu, Daidai lokacin Maryam ta iso gurin, Tadaga hannu zata kai wa Assalam duka a baya hakan yai daidai da tarewan da ,Joseph yayi sai ta samu hannun shi, Wani irin kamshin turaren,THE ne ya daki hancin ta ba shiri ta mike tsaye daga tsugun nin da tayi, Shikuma Joseph ya dago da yaron daga inda yake kwance cikin kasa, yana dan kakabe mai rigar shi da ta baci da kasa, Maryam dake tsaye tana ce mai bazakazo muje ba ko sai mun makara, Joseph yadago faren idon shi yadan kalleta ya ce ki tafi zan kawo shi, Shiru tayi tana nazarin mutumin kafin tayi kwafa ta wuce tana mai jan hannu Assalam tana gunaguni, Hannun yaron ya rike suka shiga cikin green land super market, tare can ya fito da yaron dauke da yar leda shake da kayan kwalama, Inda ya rike mai hannu zuwa inda yqga yara madu irin uniform din su na shiga, Har bakin get din islamiyar ya aje yaron inda yadan rage tsawo daidai ta yaron yana ce mai to abikina shiga kayi karatu abinka kada kaba kowa chuculate din da da biscuit, kaji, Yaron yadan kara goge busashen hawayen dake makale a idon shi da bayan hannun shi yace har da anty ko da,Issalam? kada mai kai Joseph ya yi waban karon alamar ya gaji da rigimar yaron, Yace mai duk kan su karka ba kowa, daga haka yada ya wuce shiko Assalam nata dago mai hannu, Yana komawa gurin yaji Inus nacewa wai ina Joe ya tafine, ko dai har yanzu yana gurin rigimamayn yaron nan ne,? Ganin da sukayi mai dawo wa yasa sukayi shiru, Isowar shi yayi daidai da zuwan wasu mutane su uku a saman mashi, Yan tsofine mutun biyu sai wani matashi da yajawo su, Kowa dake gurin saida yai mamakin mai yakawo tsofin gurin su, Mai mashin din ne yai ma yan dattawan nuni da Joseph yana cewa gashi nan ai, Daidai lokacin da mutanen sukayi wa wa yanda suka tarar sallama, cikin daga hannu, Sai dan shiru ya biyo bayan hakan na wani lokaci, Shima Joseph mamakin nuna shin da akayi yake yi a lokacin, Cikin mutanen mutum gufa ya fara bayani kamar haka, Malam yat uwqr muce tasa may mu da kuka dazun take sheda muna abinda yafaru, Ai duk wanda ke gurin saida gaban shi ya fadi da jin maganar mutumin Don su azaton su wani abu ne yafaru, da wata da Joseph din, Mutumin ya cigaba da cewa shi ne muke tambayar kokai waye sai wanan saurayin yace muna shi yakawo ka nan, Mu zo ne muyi maka godiya a bissa arin taimakon da kawai hajjo, Mungode kwarai Joseph yace kai haba baba aida baku taso ba wallahi da kubari kawai ba komai, Ai taimako yi wa kai ne, ba wani abu ba, Koda yake zuwan naku nan yai mun da dadi sosai Ammmm KB zo don Allah KB dake zaune a kusa da inda ya tashi ya zo kusa da yan dattawan, Joseph yace don Alkah zaka samo masu gina sai a nuna maka filin aja ma matan da yaranta daki hudu da katanga, Ai sai yan dattawan na kokarin hada baki gurin cewa Allahu Kbar, Yaro halan kai dan gidan waye agarin nan don ban mu san ka ba Wani habibu ne yai saurin cewa dan gidan Ema mai manjane tsohuear kasuwa, Da mamaki suke kallon shi gudan mutumin yace ikon Allah, Dan gidan Ema kuma tau Allah ya kyauta ,, Mungode kaji Allah ya haskkaka zuciya, dukbda bai gane nufin su ba yadai ce Ameen,,, Mutanen da zasu wuce ya basu dubu biyu yace su biya mai achaba, Sai bayan sun wuce ne yadan yi ma abokan nashi dan bayani breifly, Daga haka bai kara cewa komai ba,duk maganar da kowa keyi yana ji amma bai tanka ba, Shi baima so kowa yaji wanan zancen daya yafaru ba in badon Wa yan nan dattawan da suka zo wai yi mai godiya ba, Tun shigowar su gida, yafara kiran mummy zo kiga kayan da aka sayo min ance inci ni kadai bada kowa ba, Maryam da ta shigo rike da hannun Issalam ta wani zunburo baki gaba tana cewa wallahi anty in har Assalam na muna haka ni bazan kara zuwa dashi makaranta ba, Dariya maganar maryam yaba a yayan nata, tace idan baki je dashi ba, ai sai ya zauna dama kece mai daurewa karya ai, Nan Maryam taba yar ta labarin abin da Assalam yai masu hannu takuma mika mata ledar kayan kwalamar da aka sai mai, Uwar ta karbe ledan tana cewa aiko bazai sha ko kwara guda daga ciki ba, tunda abin da yayi ke nan, Anty Dije takarbe ledan ta shiga dashi dakin ta, Wani sabon kuka yasa yana kokarin turje turje a kasa, Maryam ce tabi bayan anty da sauri tana fadin dan Allah kiyi hakkuri yaya, Abashi gobe ba zai kara ba, ai, Da mamaki anty dije ke kallon Maryam ce ta langabe kai kamar zatai kuka don ankarbe ma Assalam kayan shi, Sai kace ba ita bace ta kawo karan shi yanzu har tana ikirarin bazata kara fita dashi ba, Murmushi tayi tana cewa kai Maryam abarki kawai daidai lokacin da maryam din ta karbi ledan a hannu anty, Ido anty Dije ta bita dashi tana murmushi acikin zuciyar ta tana yaba irin son da yar kaunar nata takeyi wa yaranta,,,,,,,,,, Afuwan ba yawa pls,,,,,,, ZEEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣ BY ZAINAB IDRIS MAKAWA 🐎HUGUMA GROUP🐎 Maryam Abdullahi bobi, diyace ga malam Abdullahi bobi, Asalin , Mahaifin su daga wani kauyen kwantagora suke wanda ake cewa kamfanin bobi, Su malam Abdullahi yan asalin can ne saida zama yakawo kakanin su a cikin garin kwantagora da a cikin jahar Niger State of Nigeria, Sana,ar maihafin su shi ne saida kayan masarufi a cikin kasuwa, Yana da mata biyu inna hussai da maman, tunga, Saidai da dadewa can ya, auri wata yar uwar shi daga bobi, saidai gaskiya babu so a tsakanin su , Don tana da wanda take so a can bobi, don haka ta tada hankalinta bata zauna,, auren bai dauki wani lokaci ba ya mutu, Ashe akwai rabo a tsakani don haka aka samu cikin maryam, Bayan haihuwar maryam ne tai wani aure anan cikin kauyen Kampanin Bobi, Tunda aka haifi maryam sau guda aka taba zuwa da ita gidan mahaifinta, Duk yarinyar na ran malam Abdullahi amma yasan cewa kawo ta cikin iyalin shi wani sabon fitina ne, Saboda sun riga sun tsani uwar Maryam har abin ya shafi yarinyar don zuwan da akayi da ita ko kallonta ba wanda yayi, Sai Dije ce kawai taita nan, nan da maryam din tana nuna kulawar ta akai, Amma a lokacin Dije tana secondary bata kare karatu ba balle tayi aure, Bayan kare karatun tane ta hadu da wani dan makwabcin su Iliyasu ma,aikacin aikin custom ne, Sukayi aure tun lokacin da dije ta tsaida miji tasha alwashin cewa za ta dauko maryam su tafi tare, Amma sai uwar ta Inna, hussai tace mata sam bata yarda diyar ta ta dauko mata, wata wahala ba can daga kauye,, Don haka Dije tabar wanan zance kamar ta fita batun sai bayan auren su da ILiyasu ne Baba yaje dakan shi bobi ya dauko maryam da yan kayan ta yazo ya danka wa Dije ita amana, Tun wanan lokacin Anty Dije ke kula da yar kaunar ta , ta cikin amana, Har zuwa lokacin da Allah yabata nata haihuwa, Assalam.shine nafarko sai Issalam, wace yanzu daga gareta ba,a kara samun wani ba, tukun har yanzu, Mijin Anty yana zaune a can jibiya ne bakin border don da lagos yake har ya taba zuwa da su sai da anty ta kusa haihuwan Assalam suka dawo, Inda mahaifiyar shi tace bata yarda ya koma da ita ba , don in yatafi da iyalinshi wai yana dadewa baizo gida ko kuma aike, Tun wanan lokacin anty ta zauna kwantagora bata kara bin mijin ta abisa umurnin uwar mijin ta, Saidai har yanzu abin bai canza ba don gwamma da da yanzu don yanzu baifi ya zo sau uku ba a cikin shekara, Saidai yakan aiko masu da sako akai akai, Maryan yanzu tana karatu ne a Girls day secondary school kwantagora, Tana Ss² yanzu su kuma yaran antyn ta sun fara nursery a wani preravent school,, Maryam ita ba fara bace kuma ba baka ba yar doguwa da ita bata da jiki tana da hanci madaidaici da ido masu dan girma,,,,, Yau kusan satin shi biyar da barin gari yana can suna ta harkan man fetur,, Saidai a kai akai suna yawan waya da abokan shi, Musan man KB da jibrin wanda dama sun fi shakuwa da su tun suna yara, Don duk irin wulakancin da ake mai lokacin suna yara na kasan cewar shi dan kirstan acikin su KB da jibri a gaskiya ba suyi mai sukan ja shi zuwa gidan su , Idan kuma mahaifin shi yasani a lokacin yai mai dan karen duka, Har akwai wani lokaci da ana bukin babban sallah yabar gidan su tun da safe zuwa gidan su KB , da kayan shi dunkule a leda a cewar shi zai bi su gurin yawon sallah ne, A gidan su anyi bidan shi har angaji kasan cewa idan musulimi suna irin wanan buki su kiristan sukan killance diyan su a gida basu bari su fita ko ina, Hakan yasa shi yin asubancin barin gida zuwa gidan su KB din, Dashi akayi ai,kin komai na naman inda aka diban mashi zuwa gida dabara yayi da zai tafi yaba KB saura yace ya boye mai Baban su KB shi yaraka shi da yaga yana labe ,labe Suna zuwa tun daga nesa uban shi yafara yi mai sababi saida mahaifin KB ya bashi hakkuri, Wucewan mahaifin su KB kadan akasamay shi akai ta bugu kusan duk wanda ya girmay shi a gidan ranan sai da ya doke shi, Yana kallo naman da yaje kwadai yai wahalar aiki aka zuba a cikin ruwan kwata aka murje, Duk da haka washe gari saida ya koma, wurin KB da zai tafi kasuwa yadan dade gidan sanan ya wuce, kasuwa,, Iya gaskiya shi Joseph yana jin dadin zaman da su keyi da su KB da sauran friends, Idan yana cikin su ana hira yakan ji kamar an yaye mai wani nauyi duk da ba magana yake yawan yi ba acikin su, Yadda suke hira ana challenges din juna ko kuma kuma yayi ta kallon yadda mutane ke ta faman zirga zirga, Abin yana burge shi so sai don idan a cikin yan uwan shi IBO yake sam babu wanan irin dabi,ar sai dai kawai kulun a na gurin bidan kudi,,,, Shidai dabiar hausawa tana mai a rayuwan shi don in ba haka ba da irin dukan da yasha yana da ya daina kula su,,,, Don haka tun dawo war shi, kasar su yake tunane da nazarin irin sana,ar da ya kamata ya jona su KB aikai wanda zai jawo masi cigaban rayuwar su Batare da,sun dogara da wani ba ko kuma da aiki gwaunati, kamar yadda akasarin hausawa ke yi yanzu, Yau da ruwa aka tashi a garin na lagos don haka duk wanda yakai wani lokaci a waje go slow ta rutsa da shi, Joseph wanda shigowar shi ke nan garin a lokacin, da ake tsula ruwan, Tafe yake a hankali a cikin motar shi yana tafiya kamar wanda bai son yin,,,, Idon shine yakai ga wani motar daukar kaya watau tirela, Wace tayo dakon buhu,hunan shikafar yar gwaunati sai,dai,duk ruwan sama yasa duk ta fara jikewa ga masu motar nata wahala, da shi Wani irin tunane yadar su cikin zuciyar shi wanda tasa shi dan yin murmushi a lokacin, Gidan shi dake cikin, Apapa ya wuce direct inda yasamu maigadin gidan yabude mai get ya shige , Mai aiki naganin shi yatashi da murnan shi yafara kokarin hada mai dan abinda zai ci, tunda yasan cewa ogan nashi baya cin abincin waje,, Yana ganin oga yasan cewa yau boza tazo don yasan cewa duk sanda ogan na shi ke gari duk kan su dake a karka shin sun yake wahalar kudi, Wanka Joseph kafin ya fito har an hada mai girki mai lafiya, Bayan ya gama ne yasamu daya daga cikin kujerun falon ya haye,,, Don har zuwa wanan lokacin ruwa ake tsulawa, agarin Don haka yana kwantawa sai shawar da zu dayayi tafado mai a rai, daga karshe ya jawo wayan shi yadan dinga dan,na wa yana kiran abokan shi daya bayan daya suna gaisawa, Daga karshe ya kira KB inda suka dan dade suna hira akan ginar da ya bashi kula dashi na yan marayu Yai mamaki kwarai da jin dan kudin da aka kashe wa ginan, Inda ya yaba da irin saukin da aka samu a wurin kayan aikin unlike irin yadda anan inda suke harkoki basu tabuwa, Don haka yai alwashi a cikin zuciyar shi zai gyara gidan mahaifin shi da suke a ciki very soon, Kafin su kashe wayar KB ke tanbayar shi ko yaushe zai shigo KG, din, Yace mai sai nan da sabon wata daidai lokacin da zasu fara yin shirin programs din su na wasan Daba da za suyi, Sun dan jima a wayar suna hira sanan suka yi wa juna sallama, suka, kashe wayar ,,, Su na sallama da KB yakira Daddy shi inda a lokacin daddy yana zaune tare da yaran shi suna hira, Mr Emanuel yaji dafin kiran da Joseph yai mai a wanan lokacin, Don dama shima yana da niyar kiran shi akan maganar ginan da yaji cewa wai yana wa wasu hausa wai da sunar tai mako, Taupa Joseph yace a cikin ran shi watau abin duniya baya boyuwa kenan, Can kuma yace ai ba mamaki don kusan shiya kuda suke da mutane dole wani zai iya fadawa baban nashi, Muryan Mr Emanuel ce tadawo dashi daga tunanen da yakeyi inda yake cewa, Joseph u, no dey hear word, I always warn u about dis people,, Jin uban ya ci gaba da fada ne sosai yasa Joseph yai sauri katse shi da ce, Dad, am doing all dis b,cos of u Saboda kai ke zama ko yaushe a cikin su indan har mun nuna cewa bamu tare da su a fili a baza mu samu biyan bukatar mu ba,, Ajiyan zuciya Mr Emanuel yayi don jin kalaman dan nashi, Shima ta fanin Joseph din sanyayar ajiyar zuciya yayi, Don jin ya ciwo kan tsohon na shi cikin lokaci guda, Bai tsaya wani dogon magana ba yai sallama da dad din, ya, kashe wayar Don gudun wani sabon magana, Rigingine ya ke kwance saman gadon sai tuna nen maganar Dad yakeyi, Yasan cewa za su kara kwasar rikici da tsohon nashi, Idan har tsohon yaji cewa zasuyi wasan nin matasan kasar kwantagora a cikin su har da shi Joseph din wanda yaba da gagarumin gudun mawar shi a taron da za,ayi,,,, Cikin, gwanin ta yake tukin motar shi daidai lokacin da ya ke kokarin shiga get din gidan su, Mahaifin shi da aboksn shi, suna zaune saman wasu benci guda biyu, da ke harabar gidan,, Cike da sanyi jiki yake tunda yai arba da su zaune suna ta dirkan giya sai shewa sukeyi a tsakanin su,,, Nan da nan maganar Jibrin yazo mai arai inda yace komai darajan mutum idan ance yana shan giya, Kimar shi da girman shi ya zube ke nan a idon duk wanda ya ganshi a hakan, Don haka sai yaji a, lokaci guda duk wanda ke gurin kimar su ta zube mashu a idon shi,, Yan samarin da ke gefe suna karta suka zo suka tare shi cikin murna da jin dadin ganin shi,,, Buth din motar shi ya bude masu suka fara jidan tsarabar da yazo dashi zuwa cikin gida, Inda dattawan ke zaune suna dirkan giya yanu fa don kwasan blessing, Kirari wani daga cikin su ke mai irin kirarin yan gidan su da ake masu a can kasar su, Jin kirarin yadan sashi yin yar murmushi daga nesa saboda yana son wanan kirarin na kakan su da ake masu, Karasowa yayi inda suke yadan yi kamar ya duka yace masu barkan ku da gida, Gabada yan su sukace mai blessing my child, Ya hanya ya ya kabaro lagos yai dan murmushi yace daga Abuja yake shine yace bari ya kara so nan,, Wani dan gajere mutum daga cikin su yadan kalle Joseph din daidai lokacin da yake zuba bommi a cikin wani cup, Yace waiting dis boy want, in dis town, no b last month i saw him,,, Baban Joseph da ya sha yai tatil yace cikin murya tsatsaye, Na, me send for him wooo, i wan tell him about d white men, Joseph da yaga kamar shirmay suke zubawa ga warin giyar bommin da su ke sha duk ya cika mai hanci, Sai cewa yayi sai anjimar ku yana kokarin shigewa, Wani daga cikin su ya dan yafito shi da hannu yana mai alamar yazo ya zauna Wani daga cikin sune ya iya bude baki yana cewa come nd join us my son, No tnxs kawai yace yana mai kokarin mikewa tsaye yabar gurin Tunda ya shiga gida baiyi marmarin fitowa ba saboda yan dattawan dake waje suna holewar su,,,, Sai sha daya na safe ya ke shedawa su KB yana cikin gari, Duk sunyi mamakin jin cewa yana gari don basu sa rai cewa zai shigo very soon haka ba,, KB ne ke ce mai ya na tafe yanzun nan, Sai Joseph din ke ce mai ya bari har zuwa yamma don dama wani program yazo yi a church din su,,,, Church kan ya ciki makil yau saboda kiran gagawa da akai ma duk wani mabiyin wanan church din Kamar irin su Joseph da iyayyen su ke ciki yazama dole su zo wannan taron da ance mai ma,anace taron, Wasu turawane ke perching kamar kuma shawa da umurni suke ba sauran mutanen, Inda suke neman hafin kan duk wanda ke cikin addinin da ya kawo gudun mawa mai tsoka Indan an hada kudin daga baya sai su shiga daji inda kauya wa suke su fara masu wa,azi da kuma jan ra,ayi da abin duniya, har su samu galaban jan ra,ayin su Ihu da murnan jin wanan shawaran church din ya rude dashi, saboda suna ganin cewa zasu iya cin galabar yan kauye da,dama a, hakan, Kafin wani lokaci an fara yawo da ture ana karban gudun mawan gurin jama,a, Wani dan kyamushashen bature ya kara tashi yace Wani hanya kuma guda da zasu bullowa al,umma dashi ita ce Suna da wani baiwa da zasu iya kara jan ra,ayin mutane da shi cewa, Duk wanda baida lafiya za su warkar dashi indan har yaji sauki to ya zama dole ya bi akidar su,,, Sannan su kara tabbatarda cewa har wa yan dake a ciki idan su na da wata cuta zasu iya zuwa a warkar amma da sun ji sauki ya zama wajibi a kara masu mukami acikin church,,, Joseph najin haka ya mike kamar mai waya a zuciyar shi yana cewa yan yaudara ne kawai da cuta,,,,,,, ZEEEE MAKAWA,,,,,,,,, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Zaune take gaban mirrow tana dressing kusan duk abinda mace zata bukata na fente fuskan zamani ta na dashi a gurin, Dogon rigar atamfa ce ajiye saman gadon ta gefe hade da dan kwalin shi da gyalen shi,,, A hankali tadauko rigar ta zura a jikin ta, ta gyara tsayuwar rigar cifcif a jikin ta , Ta mika hannu ta dauko dankwalin ta fara daurawa a kan ta, Batafi minti shidda ba taga komai takara feshe jikinta da turare,har zuwa gyalenta, Kinsan da gyale da hijab sun fi daukar kamshi a kayan mace, Saboda hatsari mace ta dinga shafa turare a jikin ta yana kawo wa mata breast cancer so sai, wlh,,,, Amma idan kin dan sa wa top din ki is ok ko ina ki kabi zaki na kamshi so sai, har na wani lokaci (pls be aware) Wasu takalma ta jawo wanda sukayi matching colour da gyalen ta, da yan kunen ta ,,,, Tsaye take gaban mirrow tana kare wa kanta kallo, A, lokacin wayar ta yai kara cikin sauri ta dauko murmushi tayi don ta san ta bata lokaci, Haba Aisha kin san fa cewa ance ba makara don Allah kada kisa a rufe get ba mu shiga ba, Daidai lokacin ta rufe kofar dakin ta, don gudun kada yan kan,nen ta su shiga mata cikin dakin suyi mata barna, A kofan gidan nasu ta iske Amina kawar ta cikin motar saurayin ta suna jiran ta, Baka jin komai a motar sai sautin kida dake tashi kamar kune mutum zai fashe, Duk inda suka bi dule a waige su don jin,karar kidan motar da ya hayhake ko ina, Tunda ta shiga motar gaisuwa kawai ya hadasu da saurayin Amina Ba su tsaya ba sai wani mating wuri da aka killance a rubuta da manyar haruffa, kamar haka, SAFARA MOTEL,,,,,, Sai wasu yan kananin gloves da ke haska wanan rubutun yana bada launi kalakala, Duk saurin da sukeyi sun makara don sun samu an rufe get, ko,,, Komawa Aisha tayi baya tadan jin gina bayan ta da mota, da sukazo da ita, Tunda har an rufe get yanzu dole sai ta samu partner da zasu shi ga, Sauriyi Amina ne keta faman zirga zirga bidan wanda yadace ya hada Aisha Sanda da shi, Sanin halinta na zama first class ya sa bai yi gigin hada ta da kowa ba, Wata mota ce ta dan no inda suke tsaye tunda ganisa kaji engine din motar kasan yar lafiya ce, Rangerover sport, ce ta dan no tun daga nesa aka kashe mai ido da hasken motar, Duk da bai san kowaye ba aciki yasan wanda yasan shine, Don haka yai tsaye guri guda har na cikin motar ya fito KB ne yafara fitowa ta gefen mai zaman, banza,sai kuma Jibrin wanda ya balle, marifin motar baya ,ya fito, Tunda ga nesa ya gane su KB don haka yasan cewa, Yanzu za ai solving din problem din su, ma,ana Aisha ta samu irin da zai hada su, Joseph ne yafito karshe sanye yake da dinkin shadda mai ruwan makuba , Sai sarkar gold da zoben gold din guda biyu a hannun shi, A hankali yake takowa har zuwa in,da su KB suke tsaye da Lawal abokin su, Hannu sukayi da lawal din inda ba bata lokaci lawal ke fada ma su bukatar shi, Ya na mai nuna Aisha inda take tsaye, cikin second duk suga wai amma banda Joseph, wanda kamar ma bai gane may ake nufi ba, Inda lawal yaci gaba da fadin sun bar pass din su, a gida ne gurin sauri, KB ne ya waiga inda Joseph ke tsaye yana kallon ya ce, Man wanan taimakon ka ne, pls Cikin nuna rashin ganewa yake kara tambayar su, komai zai mata nan dai KB yakara mai bayani, Kafadar shi dan daga alamar ba damuwa ai, Shigowan su a cikin dakin taron ya haskaka so sai don mai MC yai announcement din shigowar su kamar yadda idan wasu sun shigo ake cewa ga yan kungiyar kaza nan sun iso, Kallo ya koma gare sai kuma dan kus kus yatashi a gurin kamar yadda aka saba, inda anga kirstan na shiga cikin musullumai adinga a queuzing din su ta hanyar da bai dace ba, Wanda yin haka najawo ma su sanyin gwiwa, so sai, Mafi yawan mutane sai mamakin Aisha sanda sukeyi a cikin su ke don sanin cewa sunan ta na cikin fitattun yamatan da ke tashe agari, Kuma gashi kayan ta sundanyi shigen kala da na jikin Joseph din wanda shi bai ko dago da hakan ba, Zaman su bada wani dadewa aka fara program din bukin, Ana aka fara gudanar da abubuwan da aka tsara a gurin, Zaune Joseph yake yadan tokare habar shi da hannayen shi dukka biyu, Yana kallon yadda ake guda nar da bukin abokin su, wanda yai aure,,, Wani can wanda Joseph din bai sani ba yazo ya ja KB da hira har suka bar kujerar, Jibrin dake gefe a zaune wayar shi taikara bayajin may ake cewa don haka ya tashi yadan koma can ta waje kadan ko zai ji kiran,,, Yanzu,daga Aisha sai Joseph ke zaune, a inda aka tanadar masu, suke zaune, Daga inda KB yake suna magana ya jiyo muryan MC na cewa ana bukata Joseph da Aisha su fito su taya ango farin ciki, Saida KB ya dafe kai don yasan cewa da wuya Joseph din ya fito tunda baida masaniyar hakan,, MC nata nata abinda akace text kb yayo mai cewa yafirmta dashi da yari yar nan suyi rawa, Kamar kada ya tashi sai yatuna cewa bazai kyautawa angon ba inda har bai fita ba don haka ya fara mikewa batare da ya kalleta ba yace mata sai ki tashi mu fita ko, Ba wani rawa sukayi ba sosai amma anji dadin fitar nasu don Joseph ya nuna kulawar shi ga ango,, Wasu yan mata dake ge fe zaune suna kallon yadda ake ta Su ka fara yan suraitai kamar haka, Au dama wanan ba musullumi bane ke inji wa ya fada maki, Dayar tace bakiji lokacin da ake cewa ana son Yusuf Joseph yafito tare da,Aisha sanda Sai gudan tace kai amma anyi harasa wallahi guy kamar wanan kuma bai sallah, Dayar tace gaskiya ni saima kawai naji haushin shi ya kamani wallahi, ita kuma Aisha don kwadai sai wani shige mai take ta yi, Wace ita ce cikon ta hudun masu hiran da tun da suka fara zance bata ce kala ba, Tace kai ku dai na daukar wa kan ku wahala ma, Iyaka,ku da shi kuyi mashi fatan alherin shiga cikin islama indan har yana da rabon shiryuwa, Allah yasa yagane gaskiya yadawo hanya, Sai ta farkon tai caraf ta ce a haka ? Wanan ai yai nisa baya jin kira, in bashi ba ai tun yana yaro da ya musulunta, ko,,,,, Ita dai wace bata maganar sai cewa ta yi ai abin daga Allah ne kawai, in Allah ya nufe shi da shiryuwa saiko ya shiru, yadawo hanya, Haka dai kusan ko wani kujera suke ta zancen su kamar yadda gurin buki ya tana da Kai kana kallon wani wani yana kallon ka, Ganin cewa dare ya fara yasa Joseph yai su KB magana akan cewa su zo su tafi don shi baya yin dare sosai a waje, Don duk haka tarbiyar yaran IBO suke duk ganin kada su basu yarda,su kai karfe takwas na dare waje, Wana na daga cikin irin tarbiyar da suke wa yaran su, Idan kuma sana,a ce bakin karfe shidda andawo gida ke nan daga gurin sana,a, Saidai kuma tun karfe bakwai na safe anbar gida ke nan zuwa gurin bidar kude, (Allah ya kyauta) Wanan haduwar da Joseph yayi da Aisha itace silar haduwar su, Don tun a gurin da ta ce ya ara mata waya takira kawar ta don su wuce tasamu nobar shi,,, Da zai tafi ma lake mai tayi akan ya bata lift zuwa gida saboda dare yayi a cewar ta, Anan yabar su KB daga shi sai Aish sanda suka kamo hanyar zuwa gida, Da kwatance tai ta yi mai har suka iso gidan su, Aisha din, Koda ya Parker motar shi bai ce mata komai ba sai jiran yakeyi tafi ta yasamu ya wuce Ita ta tsaya wani yanga kamar wace bata da lakka ajikin ta A hankali ta dan waiga inda yake tana cewa nagode fa,sai wani lokaci ke nan kuma , Kai ya kada mata yana mai cewa No ba matsala ai ,, Tana fita yafigi motar shi da karfi yabar uguwar zuwa, gidan su,,,,,,,, Gudu yake shararawa a motar shi tanyar ta zuwa kudu, don kirar da yasa na gagawa daga abokan sanar shi saboda meeting din da zasu yi don kara wa mai farashi saboda harajin da gwaunati ta saka masu, Shi kadai ne a cikin motar sai kidar da ya sa nawakar wani dan yaren su inda yake wa egwaii of Benin kirara, Wayar shi dake gefen shi tai babirashon, hannu ya mija yadauko wayar hankali shi na saman titin kadan don yafara jin kamshin okene, Ganin bakuwar noba yayi acikin wayar shi dan mamaki ya baiyana a fuskan shi kadan, Don gani bakuwar nobar kuma yasan cewa wanan wayar sai special mutanen sa ke kiran shi da ita, Kamar ya aje saidai ya dauka yana mai karata a kunen shi, Muryan mace yaji tana mai sallama a cikin hausa, Cire wayar yayi yadaga yana kallo don shi a bin ya bashi mamaki so sai wallahi, Sai kuma yace kila wrong noba ce, Karakara wayar yayi a kunen shi don yace is wrong noba, Saida abin mamaki daidai lokacin da ya kara wayar akunen shi a lokacin ne, yaji mai maganar tana cewa Yakake Joseph ? Mamaki karara a fuskan shi ya ansa mata da lafiya, Wake magana ya ke tambaya cikin mamaki, saida tai yar murmushi har yana jinta daga inda yake Tace kana magana da Aisha Sanda ce, Aisha Sanda ? Joseph ya kara nanata sunan cikin mamaki a fili Tace mai eh Wace kuka hadu a wurin dinner din hamza har ka kaini gida, Ok ok yace nagane ya kuke ta amsa mai da lafiya lau, Yau nake tambayar KB kai yace min ka wuce sai tadan shake muryan ta kamar mai shirin kuka, Tace shine bakazo munyi sallama ba katafi, ? Maganar ta ba shi mamaki sosai don dai ya san cewa bawai wani sanin juna sukayi ba ko sabawa, Amma sai kawai yadake duk da cikin mamakinta yake , ya ce , mata just sorry, Kamar ta na ganin shi kai kawai ta gyada mai kamar yana ganin ta a fili,, Wani irin ajiyar zuciya yayi yana mamakin maganar ta acikin zuciyar shi,,, Ita ko Aisha wani irin shu,umin murmushi tayi bayan sun aje wayan azuciyar ta tana kiyasta abinda, take planing akai,,,, Tsaye yake a cikin wani ma,aikatar tatan man petroleum, da ke kudu, yana son idon shi ya tabbatar mai da ko mota nawa daga con n motocin su , suka shigo, Wayar shi tai kara noba ce ya gani babu suna don haka bai san mai wanan nobar ba, Yadauka yana mai cewa hello, Aka ansa mai adayar bangaren, jin muryan mace kuma ba hausa tana cewa Hello mun wuni lafiya ya kwana biyu ? Hello wake magana yace Mamaki ne ya kama Aisha jin cewa har yanzu ashe bata shiga ba, Ansa mai tayi da cewa Aisha ce daga KG, Dan shiru ya biyo baya kadan sai can yake ce mata ok nagane Pls ki bani dan lokaci zan kira ina aiki yanzu pls Ba matsala race tana mai aje wayar cikin jin takai ci, Amina wace ke kwance gefen ta har tagama wayar ta numfasa tace wallahi Aisha kina bani mamaki Cikin dan jingina bayan ta da bangon dakin da suke zaune tace agani ki ko, Amina tace a ganin kowa ma, Kin fasan cewa ba musulmi bane wanan guy din don may zaki nace a kan shi dole sai kinyi halak da shi, Daidai lokacin ta dauko wani abin gyara kumba daga cikin jakar ta, Tafara dan kankare kumbar hannunta da abin sai can kamar bazatai magana ba tace Kina nufin don ba musullumi bane bazan yagi rabo na ba ke nan, Cikin mamaki kawar nata ke kallon ta don Aishan ta ba ta mamaki kwarai ta ya zatai mu,amula da wanda ba musullumi ba, Gaskiya ita bazata iya ba, iyakar harkan ta ga musulumai yan uwanta,,, Saboda yawan matsin da take mai dole yafara dan sakin jikin shi da ita har suna dan hira jefi jefi a waya, Tafe take ciki uniform din su na girls day secondary school, sauri takeyi don ta isa gida, saboda ta samu ta shirya da wuri zuwa islamiya, Don a kwaita da tsoron bugu bata son abinda ya tabi lafiyan jikin ta sam Wasu "yan matane mutum biyu cikin shiga ta isa da nuna lokaci ke tafiya, Tafiyar ta takeyi cikin sauri yasa sukayi kusan yin karo da daya daga cikin yan matan ne tai karfin halin cewa haba malam wani irin tafiya ne kikeyi babu ko tsari balle ki nuna ajin cewa ke ma mace ce, Maryam wace duk saurin da takeyi bai hana ta tsaya wa guri guda ba cak,,,, A hankali ta juya inda suke tadan kalle su murya a raunane tana mai cewa kuyi hakuri pls ban san cewa gurin ba zai muna bane, Daga haka ta juya batare da ta kara cewa uffan bata ci gaba da tafiya sai dai maganar na kona mata zuciya, Don may zasu ce ita bata da aji kodon batasa bujen da ya manne mata jiki bane, shine rashin wayewar da suke hange a gareta, ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Kusan duk wanda ke cikin wurin yana saye da rigar coat ce a jikin shi sai yan kali lqn ne ke da shiga irin ta hausan arewa ko su basu mutum uku ba daga cikin su,,, Daga ni meetings suke yi kuma meeting ne ma tsauri don duk kan su fuskan su babu wallawa a ciki, Kadan kadan hayaniya ke dan biyo baya musan man idan an fadi wani abinda ba,a yarda da shi ba agurin, A wajen harabar gurin kuma maza ne kaitai majiya karfi kashi, kashi, da alamar security ne su Sai wasu irin manyan motoci da sai inda idon ka ya tsaya,,, Kowani kusurwa na wajen an zuba jamian tsaro birjik Sunan mutum uku ne yanzun haka ake muhawara akai, Mr Inok ,Ishaya noma sai Joseph,Emanuele, Daya daga cikin su ake son ajewa a matsayin sectarianism din su na matasa masu harkan man petrol, Daga karshen zaben ya fada akan Joseph wanda akasari mutane ba,su so hakan ba ,,,, Wani dan Jos suka so Ishaya Noma, Wanan mukamin ya jawo mai ci gaba sosai tare da duk wani wanda ke kusa da shi, Abokan shi dana sanar shi sun hada mai party samun cigaba, Mutanen kwantagora sun zo mai murna, don kusan duk, yan abokan su sun zo, Wanan zuwan ya tayar masu da hankali so sai fiye da tsab manin su, Don duk daukan da suke mai ashe yafi da haka a fili, Sai bayan sun wuce ne Aisha ta samu wanan labarin kuma har an tafi, don haka ta lalashi Amina har ta yarda suka shiga motar kasuwa suka tafi har can, Bayan sun isa ne, takira nobar KB take sheda mai cewa gasu sun iso garin, KB yai mamakin jin wai ga su sun shigo cikin garin Inda Joseph yake cikin abokan harkan shi KB ya rutsa yaje har cikin kunnen shi yai mai rada yaba sheda mai zuwan su Aisha Sai da Joseph yadan nuna kaduwa don bai taba tsan manin zuwan su ba, Wani yaron shi yakira yai mai nuni da KB yace su je tare azo da, su masauki Su kan su sun yi mamaki kwarai da irin masaukin da suka samu,, Washegari ne zaa ,gudanar da taron tayar murnan samun cigaban da su Joseph suka samu, Inda taro yai taro don duk bakon daya zo dana kusa dana nisa Joseph yasa an karama shi da wada tacen abinci da na sha daidai gwargwado, Fili na musan man yasa aka bawa abokan kurciyan shi a ce war shi, inda suka fito cikin musulunci tare da hasken musulunci a fuskan, Sai mamaki su akeyi yadda sukazo taya,shi murna haka da yawa, Anyi yan wasan ni da kuma raha kamar yadda akanyi inda wani abokin kasuwan cin shi da Lagos ya ba shi shawaran yai aure, hakana tunda Allah ya,wadata shi da arziki tun yana yaro,,, A haka taro ya,watse , wa yanda suka zo daga nisa suka fara niyar komawa gida, Sai, a lokacin Joseph yasamu kebewa da su Aisha cikin yar sakin fuska yake masu maganan,,, Inda yai mata godiya sosai da kuma bata, appointment, nan da two weeks zasu hadu, Aisha taji dadin wanan tafiyar da sukayi saboda irin guzurin da suka dawo dashi, Tun wanan lokacin ya rage samun lokaci kamar da, yanzu ya kwana biyu baizo kwantagora ba duk da aiken da mahaifin shi Mr Emanuel ke mai na cewar church members na son ganin shi, Aiki yakawo shi Abuja don haka yai amfani da wanan damar ya iso amsa kiran mahaifin shi, Yan church din sun gudar da,addu,an su gare shi tare da fatan alheri zuwa gare shi, Yaji dadin wanan adduan da akai mai don haka yaba gagarumin gudun mawa a church din nasu, Tun jiya Sunday da suka dawo church din bai kara fita duk da yawan wayan da friends din shi keyi don jin cewa yana gari, Bai samu fitowa sai bayan karfe biyu inda yace ma KB yazo su fita, Don motar shi ta na bukatar, wanki sosai, don haka, yabar ta kanin sa ya fita mai da ita gurin wanki,, A,saman mashin din KB suka fita, fitan da yasa mutane suka san cewa Joseph yazo gari, Hmmm Dan Adam da kudi, kafin wani lokaci har yan kai koke sun isa gurin da suka san cewa zasu ganshi su yi maula, Mutanen mu ho, idan zuciya ta mutu koma mutum na iya yi don kawai ya samu kudi, Sai bayan sun gama maula ne sai a koma gefe ace ai dan kafirin nan yazo Ai yanzu ba asan sanar da yake yi ba sai dai kudi ake ganin shi da shi ba a san ida yake samun su ba, Wasu kuma, cewa suke yi ai Joseph mafiya yake yi yanzu sosai, irin na ya birni wanda ba,a gane akidar mutum,,, Maryam tana tsaye a gaban mirrow tana gyaran hijab din dake a wuyan ta, Issalam tazo ta bayan ta ta rugumay ta , Issalam kada fa ki sa in fadi kasa wqnan rikon da kikai min,,, Yar wasan kokuwa suka fara yi da Issalam din kama ba zasu makaranta ba, Anty Dije ce ta leko dakin jin su shiru da tayi dakin, Cikin mamaki anty Dije tace, amma dai, maryam anyi uwar banza Yanzu ku shirya ku wuce shine zaki buge da wasan kokuwa da Issalam, Maryam na dariya daidai lokacin da Issalam ta kara kai mata damka ta na ko karin wai sai ta kayar da maryam a kasa, Daidai tana fadawa kan katifa, tace ma yar nata ai yanzu zamu wuce insha Allah,, Anty Dije na tsuki ta sake labulen dakin tace ai ku ,za,a daka a makarantan, Har ta kai kofa ta tuna Assalam baya dakin kira ta kwada mai, Daga bayi ya karba mata mama gani nan ina wanka, Cikin mamaki jin cewa yana cikin bayi har yanzu yasa anty mamaki Hanyar bayin ta nufa don ganin may yake yi a ciki har yanzu, Sabulu yasa a fuskan shi dumu dumu, bai ko san shigowar uwar tashi ba ciki, Sai lokacin da yaji hannun ta a jikin shi ta danko shi, Wani irin ra,zananen ihu, yasa wa uwar don yana ganin kamar zata buge shi, yasa yaron yaka ihu, Daga, maryam har Issalam duk bayin inda yake kwala ihun suka nufa, Wanka su ka samu Anty Dije tana mashi yana ta kokarin kubcewa, Bayan sun shirya ne suka wuce islamiya saboda sun makara, yau Allah ya taimake su ba su sami malam babba yadan fita don haka badu sha duka ba,,, Isowar su Joseph da KB a majalissar su ya yasa gurin yadan kaure da hayaniya cikin dan lokaci kadan,, Bayan dan gaishe gaishen da ya biyo bayan ne suka samu guri suka zauna Fira akeyi amma shi Joseph uffan bai ce masu ba sai dai idan anyi abin dariya shima yadara, Ana cikin hirane daidai lokacin da yan makarantan Isalamiya suka fara tasowa, a lokacin wayar shi tai kara alamar kira yashigo mai, Aisha ce ya gani baro baro a jikin screen din wayar tashi, Dan tashi yayi nisa kadan daga ind suke zaune, don ya karba wayan nata,, Tambayar shi take yi yana ina ne ? Don tana son ganin shi ne, kafin yabata ansa sai ji yayi an rike shi ta bayan shi, Da alama kuma dan karamin yaro ne don daidai iya gwiwar shi yaron ya tsaya, Kafin ya juya lokacin da yaji haka yake cewa Aisha yana zuwa pls, Waigowa yayi a hankali yana kokarin ganin kowaye yaron, Wani dan farin yaro yagani ya rike shi tsab yaron na cewa, Abokina kullun sai na diba ko zan gan ka idan zamu tafi islamiya amma bana ganin ka, Idan kuma na tsaya sai little, mum ta dinga zagina, Rage tsawo Joseph din yayi don dai bai fahinci ko may yaron ke tawa bayani ba, Maryam, dake tsaye gefe iyakar kuluwa ta kai har tafi nan, Don ji takeyi yau idan ta fara dukan Assalam bazata daina ba tunda har yasa ta tsayawa daidai gurin yan sa idon mutanen nan, Hannun Assalam Joseph yakama ya hade guri guda yana mai fuskantar yaron, Kafin yai magana sai muryan maryam suka ji tana cewa Assalam bazaka zo mutafi, ba ko, So kake dare yai muna a hanya kafin mu isa gida ko, Nunata da hannu Assalam yayi yana mai cewa dakace kada in basu sweet dina sai da little mum ta ba Issalam tasha, Joseph dai har yanzu bai fahinci yaron ba don ya manta cewa sun taba haduwa da yaron ,,, Yace wa Issalam bari ,zan saya ma wani mai yawa amma kaba kowa yasha kada kayi rowa kaji,, Jibrin dake kallon draman su tun dazu yadan taso daga inda yake saman wani benci yana cewa cikin turancin Ai yaron da ka taba dauka ne da ya fadi a gurin nan da zasu tafi,makaranta, Saida yadan yi tuna ne sannan yace ok ok na tuna a haba dai my friend kaine haka kazama big guy,, Yakara jawo yaron zuwa cikin jikin shi ya rungumay yadan dago kai yana kallon jibrin,, Yace wanan yaron baya mantuwa pa kadiba bafa yau ba wanan event din ya faru wai ama ace bai manta ba, Maryam kuka kawai ya rake tayi a lokacin saboda sukuwar da yayi da Assalam, Cikin zafin nama ta isa inda suke tana kokarin finciko Assalam, din, Kai Joseph yadaga yana kallonta yana cewa haba barshi mana pls, Wanan yaro ne fa shi ai baisan komai ba, yana fadin abinda ke a mind din shine fa kawai, Batare da ta saurari may yake cewa ba tace kazo muje gida kaji wallahi yau sai na ma mugun bugu Assalam, Jibrin da baiyi magana ba tun dazon ne yake cewa kutafi zan kawo shi gida, Cikin mamaki ta dago kai tana kallon mai magana don ita a iya sanin ta bata taba ganin jibrin a gidan nasu ba, Yagane kallon da take mai don haka yace mata ke wanan yaron fa nima yaro na ne kin ji, Kafin mamakinta ya kai karshe Taji yana cewa ke ba kaunar matan Isiya Custom bane, Kai kawai tadan gyada mai alamar eh ita ce, din Yace to kutafi kawai zan kawo shi, Still wani irin mugun kallon see u tai ma jibrin din alokacin, Yace ke nifa yaron gwago laure ne don haka ki wuce kawai, Jin an ambaci gwago laure yasa maryam fara kama hanya rai bace hannunta rike da Issalam tana ja kiiiiiiii, Anty tana kokari kauda abincin dare daga dan matsakacin kitchen din ta taga shigowar marya da Issalam a hasale, Babu Assalam a tare da su hankalinta na kofar hanyar shigow taga shigowar Assalam din, Kafin yatambaya maryam tace wallahi Anty gaskiya ba zan kara fita da Assalam ba tunda a gaskiya duk zamu wuce sai yabani kunya a hanya harda zuwa rokon fa naji yanayi, Ido waje Anty Dije tace roko fa maryam ina yake in ci abu kazan shi,,, Maryam tana kokarin shiga daki tabar Anty Dije a tsaye tsakar gida daidai lokacin da tace ya na can mana, Idon dayafi na dazun fitowa waje tace can ina Maryam,? Tare da wa yanda yake rokon ta fada kai tsaye kawai, tashige abinta, Wuf Anty Dije ta bita ciki daidai lokacin da Maryam ta kwabe, hijabinta daga kan ta tace mata tare fa dadan gidan gwago laure suke, Wani cikin su? Kenan inji Anty Dije Uhumm nima ban san sunar shi ba inji Maryan, Hijabin da Maryan ta kwabe Ànty Dije ta jawo tana kokarin sawa, Daidai lokacin da sukaji ana sallama alamar shigowa cikin gidan Karar takalman Assalam ne ya sanar da su cewa tare da mai sallamar yake tafe, Assalam agaba da gudun shi cikin walwala da zumudin ya bude ledar dakw hannun shi Anty Dije tai saurin kai mai duka a hannu ya wurgat da ledar ya, koma baya da sauri ya fara kuka, Jibrin ne yace ma Anty Dije haba dai madam ya zaki buge shi tunda har kin gan mu a tare, Cikin yar dariyar da batakai cikiba take cewa jibrin wallahi jibrin yaron ga baida dabiar kwarai, Rokon ku fa yayi, Nan da nan jibrin yakai kallon shi ga kofar daki inda Maryam take tsaye tun shigowar su,, Hmm kawai yace yana kojarin komawa ya kamo hannun Assalam din Bai roke mu ba yadai fada muna cewa wanan time din da aka saya mai sweet saida akaba kaunar shi, Duk da joe yace kada yaba kowa, Daga Anty Dije har Maryam duk sai jikin su yai sanyi, Nan dai jibrin yaba Anty Dije labarin yadda akayi tun ranan farkon haduwar su da Joseph din Joseph da ke waje tsaye yaga Assalam ya firo yana kuka riko mai hannu yayi yana kokarin lalashin shi, Daidai lokacin Anty Dije da jibrin suka fito daga cikin gida, Tana daga ciki kadan suka gaisa da Joseph din tana mai yi mashi godiya, Yace kai haba ai ba komai bane wanan yaro ne Assalam bai san komai ba, Jin hausan shi da Anty Dije tayi yasa ta gane cewa ba bahaushe bane shi, Saidai sam batakawo cewa shi Christian bane, shi, Joseph yace wa Assalm yai shiru zai sayo mai game da mota wasan yara,,, Hakan yasa shi komawa cikin gida da sauri don yafada wa little mum da Issalam cewa za,a saya mai mota,,,,,,, ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Duk wani members din churching Catholicis suna zaune a gurin meeting din da,suka gaiyaci Mr Emanuel, Bayan pastor yayi gyaran murya alamar kowa ya yi shiru Gaisuwa yafara kamar yadda sukeyi idan anyi wanan taron, Shiru gurin yayi nawani dan lokaci can pastor yakira sunan Mr Emanuel alamar suna da magana dashi ke nan, Hakan yasa Mr Emanuel ya maida hankalinshi da kyau don jin abinda za,a fada, Wanan taron munyi shine saboda kai da dan ka, Kai kawai Mr. Ema yadan kada alamar gam suwa, Yaron ka alamun sun nuna muna cewa baya son hurda da yan uwan shi Christan Sai yaran hausawa wanda muna gudun hakan ya jawo muna abin kunya nan gaba , Hannu Mr Ema yadaga sama yai wani kyatawa yai round da hannun a kanshi yace Kai abomination, god forbid, Ya buga kafarshi a kasa Yace dat will never happen Never pastor never, Nan da nan jikin shi ya dauki rawa yana cewa imba Never sai kafa da yake kadawa ya tabure fuska dagani duk ran shi a bace yake kamar zai fashe,,,, Suma wurin sauran mutane sai fadin ra,ayin su sukeyi akan zance, Wani daga cikin su ne yamike inda yai yar gyaran murya yana cewa yana son cometi su ta diba da kyau tai nazarin ko waye Joseph,,, Yace shi a nashi halin Joseph ba zai yi haka na ba ,saboda yana da tunane so sai, Yace ai akwai wa yanda suna da kudi sosai daga cikin su amma idan anyi la,akari ko Church ba su zuwa yanzu, Amma shi in har yana gari yana attending din Church tare da su,,, Shi a ganin shi rayuwar shi ce hakana ta taimako mutane, Saboda in sun diba ai yanuna wa yanda ke zaune saman benci tare da su da hannu yace, Joseph na nin su har gida ya tai maka masu time to time, Yace ko ba haka bane, sukace gaskiya ne, hakane, Yace to shi yana ganin cewa wanan halin nashi haka take duk wanda yake tare da shi yana taimaka mai, Mr Ema dake gefe yatokare hannun shi da sanda hular shi ta gwalmade gefe guda sai kafa kawai yake buga wa a kasa, Jin jawabin na Mr Okarpo yasa gurin ya kara daukar hayaniya, so sai wanan karon, Mutane da yawa daga cikin su suka kawo shawaran cewa Joseph yaron kirkine, Shi yasa yake tare da duk wani wanda tunda suns tare ,, Don ya na taimakawa hausawa ba shine zai sa a ce yana son yin wani abinda ba daidai ba, Amma duk da haka su elders zasu kirashi su tsawata mai akan hakan, Da wanan shawaran taron ya watse kowa na fadar albarkacin bakinshi,,, Tunda Mr Emanuel yadawo daga gurin meeting din rayuwar shi take bace saboda shi a ganin shi an wa dan shi kullin sheri Saboda kawai cigaban da ake ganin ya samu, In bashi ba taya zasu dangata shi da wani akida cen, Yan uwan shi kaf ba musulumi ko wani akida ta daban, In ma hakane zaiwa Joseph din fada ya daina shigowa kwantagora gaba daya, Yana yi yana tula giya a cup yana shan ye wa kamar wanda bai da kimar ciki,,, Duk wani abinda zata bukata ta shirya shi a cikin dan kit din da tadauka don tafiya, Batare da ta fadawa koda Amina ba zatai wanan tafiyar da zatayi yau, Saida ta gama shirin ta tsab sanan ta fita tsakar gida inda, inda inna ke zaune bakin murhun ta na kasa tana gyara wuta ga koko a cikin wani dan roba mai marfi wanda ke nuna abinda ke a robar fili, Ganin Aisha waje da safen nan yasa inna cewa, wa azubo maki kokon ne ? Tawani ya mutsa fuska kamar wace akaiwa tayin kashi tace kai haba inna da safen nan haka, Kujera ta jawo gefen inna ta zauna tana fada ma inna cewa zata kauye gurin kakar su ta dibo ta, Shiru inna tayi cikin zargi take kallon yar nata wace ke magana cikin matse fuska sai kace aiba uwar ta take zance da ita ba, Har ta mike uwar tace kwana nawa zakiyi saida takai kofan dakin ta ce batare da ta waigo ba, Sai lokacin da kuka ganni kawai inna, Daga haka tashige tadauko dan kit troler din da ta shirya kayan ta aciki,, Tashan hanyar BCG ta nufa tana zuwa ana cewa Minna Abuja kaduna, Abuja tace kawai kai tsaye aka karbi dan troler kit din ta a ka nufin motar dake kan layi,,,, Musalin karfe ukun rana ta isa Abuja, wayar ta taciro takira layin shi, Kira nabiyu yadaga layin yana mai cewa hlo, cikin wata irin murya ta ke magana kamar ta mai shagwaba, Joe gani a Dikko fa, Cikon mamaki yace mata Dikko fa Aisha tace mai eh , Kwatancen inda zata sauka, ta, tsaya yai mata, yace zai turo azo adauke ta, Joseph yayi maki kwarai da jin cewa wai gata a dikko, bayan jiya sukai waya yake ce mata yana Abuja yazo yin wani dan aiki ne , Sai gashi kawai yana fitowa daga gurin meeting kiranta ya shigo mai, Wata mota mai kama da, Box ta faka a gaban ta kau da kai tayi kamar bata gasu ba, Sai hon da taji yai yawa yadan sata waigawa, driver motar ke ce mata itace Aisha ko ta karba mai ya nuna mata complement card din Joseph Hskan yasa ta yarda da shi ta shiga motar bayan ya bude bayan motar yasa mata kayan ta ciki,,, Wani gida mai hawa biyu suka shiga gidan bawani fadin fili ke gare shi ba amma ko kafin ka shiga kaima kasan cewa hadaden gida ne, Da,sallamar ta ta shiga don duk ta rude da gani daular duniya da ta gani, Jin da tayi yana ce mata hy Aisha,,u are, wel,come, Daidai lokacin da yake saukowa daga steps din gidan, Yar murmushi ta sakar mai tana wani nuna kamar alamar jin kunya, Zuwa yayi inda take tsaye yai dan hugging din ta yana mai ce mata bukin surprise ke nan, Kujera ya nuna mata ta zauna daidai lokacin mai aikin shi yashigo dauke da trey da drinks a ciki, sai cups guda biyu, a sama,,, Shi da kan shi Joseph din ya zuba mata drink din a cikin cup dai dai lokacin kuma yake tambayar ta ina kawar ta wanan karon, Tana karban cup din da yake miko mata ta ce, ba wanda yasan cewa nazo gurin ka fa, Cikin nuna mamaki yafada cikin yar muryan nan tashi, yace saboda may, Ta dan daga kafadar ta tace Just, Tace ban son kowa yasan cewa nazo gurin ka, shi yasa tadan kare zancen acikin yar shagwaba,,,, Bayan tai wanka ta kimtsa jikin ta wani dan kwalba ta dauko a can kasar handbag din ta, Wani dan ruwa ne aciki blue kamar ruwan turare ta dan shafa kadan a saman maranta, Sai kuma saman goshin ta daidai tsakiya ta man,na kadan, Body spray ta feshe jikin ta da shi mai mugun kam shi na , Wani ribon ta dauko daga cikin handbag dinta, tadan feshe shi da kamshi ta daure kanta da shi,,, Duk da tana da gajiyar tafiya a tare da ita, hakan bai hanata binshi zuwa cikin gari ba, Sahad store ya nufa da ita inda ya bata damar daukar duk wani abinda take bukata yakuma ce mata kada taji komai,, Cikin yar kunya take zabar yan abubuwa kamar wace bata so, Joseph na tsaye gefe yana kallon ta, Ganin zata bata mai lokaci yasa shi kwasan mata abubuwar da mata ke yawan amfani da su, Kamar su manshafi turare, kayan makeup, sai kuma ya juya yanufi fannin sutura, Sayayyan alfarma yai mata,a wurin sai turamen zannuwa da ya jido kamar mai hada kayan lefe, Jin bills din kudin saida ya sa Aisha dan kaduwa amma sai taga kawai ya biya batare da jin darrr ba, Mamaki fal a zuciyar ta don bata taba zaton koda quarter haka ba, daga kowani irin mutum, Sai wurin kayan kwalama da suka nufa inda nan ma ba karamin kudi ya kashe mata ba, Wani Guy dake gefe ya ya matso kusa da inda suke tsaye yana cewa sannun ku da,zuwa ya hanya, Idan kuna son dinki express ga shagon mu nan zaku samu zuwa gobe insha Allah, Joseph ya dan kalli inda Aisha taja tai tsaye yana mai tambayar ta tana bukatar dinki, ne, kai ta gyada mai alamar eh Cikin turamay da suka sayo suka bada guda biyar, dinki, akan dubu Ashirin, Babata lokaci ya biya guy din sai yabasu nobar da kuma, card wanda zasu zo karba, Daga haka suka wuce zuwa gida da kaya niki niki, A,falo suka zube nan mai aikin gidan yakawo masu plate, tare da drinks da su, cultularies, A hankali take komai don abinda take gani ya wuce tsanmanin ta,,, A daki guda suka kwanta ita, da Joseph duk yadda Aisha take ganin ita yar bariki ce ta katsewa wa Joseph, Saida ta kwana da dimbin mamakin irin halin Joseph , Duk yadda taso tambayar shi ba fuska saboda bala,in kwarji da yake mata, a idon ta, Kwanan ta hudu Abuja tare da Joseph iyakar shi da ita romance kawai da nuna concern a kanta, Kamar yadda ba ta fadawa Amina cewa ta na, Abuja ba shima Joseph, din bai fadawa kowa zancen zuwar ta ba, gurin shi,,, Mota ya bayar aka,dawo da ita har kwantagora, tare da kaya da ya saya mata, niki niki, ,,, Wa,iyazu billah yar musulumai zamani ke nan babu ruwan da dataraiya da kowani irin mutum ita dai kawai ta samu kudi shine gurin ta, Yadda ta canza kawai yasa Amina gane cewa gurin Joseph ta tafi, Cike da mamakinta take kallon ta don ganin irin abinda take fitar wa, Cikin dan rada take, cewa Aisha mutumiyar har kin fara bani tsoro wallahi don kin wuce sani na, Tana kokarin jera, kayan makeup din ta a mirrow dakinta ne tai yar dariya, tace da nai may fa,? Haba haba inji Amina Aisha ace har kuma Royce din mu ya wuce ga hausawa musulumai yan uwan mu ya koma ga Christian, haba dai haba gaskiya hakan baiyi ba, Wani irin kallo ta watso ma Amina daidai lokacin da ta bude akwantin da tashigo dashi, Kayan da Amina tagani ciki fam shi yasa ta kara zare ido waje, Tace, shin Aisha kina nufin ,,,,,, nuna kayan tayi da dan yatsanta don tama kasa furta ko a, Kwarai kuwa inji Aisha tana mai gyada ma Amina kai, tace Uban wa zai bani wanan koda kuwa sau nawa ina bin mutum motar shi ko wani mafaka Amma kinga wanan tana nuna kayan da hannun ta tace a free wallahi na,samay su Amina,,,, Ido waje Aminat ke kallonta cikin mamaki tace a free fa ? tace wallahi ko, Amma dai gaskiya mutane ba zasu gane cewa babu wani alaka atsakanin ku mai zurfi, Ina ruwana da mutane inji, Aisha, duk abinda zasu fada suyi ta fada mana, Manja da doyan da Irish da, tazo dashi ta dibar ma Amina mai yawa, Ita dai Amina sai mamakin kawar nata takeyi kawai, Ace yanzu har da arna suke mu,amula, kai gaskiya Aisha tayi nisa wallahi,,, Don haka, taja bakinta tai shiru kawai batare da tafadawa kowa,ba ita dai tasan cewa duniya ce zata fada ,,,,, Tsaye yake yana waya da kanin shi, Samuel wanda ke zaune tare da baban su a kwantagora inda Samuel ke fada ma Joseph meeting din da elders sukayi a kan shi, Yai mamaki matuka da jin zancen Samuel din don yasan cewa yana ikar kokarin shigurin ganin cewa ya kyautata wa Church din na su, Badon komai ba saidon kawai ya kare martaban gidan su daga alumar su, Cike da mamaki yasake tambayar Samuel labarin mahaifin su, Dan shiru Samuel din yayi kadan kafin can,yace yana nan saidai gaskiya maganar tadan tayar mai da hankali,shi, Kai kawai ya girgiza yana mai shafan fusakan shi in akwai abinda ya tsana yanzu shine yaga bacin ran mahaifin shi,, Sallama yayi wa Samuel din yana mai jin haushi elders din na su, akan jefa mai mahaifi cikin damuwa, Shin ina ma ruwan su dashi dazasu sa mai ido a harkokin shi, Yasan cewa koda ya kira mahaifin shi ba wani maganar da zai ji a gamay da elders din, A karshe ma yana iya ganin laifin Samuel da ya fada mai, zancen, Tun yana tuna zancen har ya share maganar, gurin fridge ya nufa yadauko goran ruwa, ya tutula ma cikin shi,har saida ya zuke gora guda gaba daya ya wurgat da rubo, a dustbin, Kiran wani Michael ne ya shigo mai a lokacin inda yake sheda mai cewa yason su hadu saboda maganar man Gas dayake son suyi a lokacin, Michael mutum ne mai iyali shi duk da bawani babban mutum bane sosai, Yasamu Michael da yaran shi suna wasan basketball, agidan shi Yaran naganin shi sukayo wajen shida gudu suna mai oyoyo, Rungumay su yai cikin jikin shi ya na dan shafa masu kumatun su, Sun san zuwan shi gidan su alherine don haka ledar Sweet din da ya riko masu ya mika masu, Murna da ihu suka hau yi suka shige cikin gidanan su binsu yayi da kallo Nan take alkawarin da yaiwa Assalam ya fado mai arai, Don yasan cewa yaro baya man,ta alkawari duk lokacin da yaga wanda yai mai alkawari bai cika ba sai ya tuna,, Don haka ya kudurta a ranshi cewa da yabar gidan mic zai wuce yaiwa Assalam sayayan shi ne,,,,,, ZEEE. MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Yau gidan Anty Dije baka jin komai sai kamshin girke, girke ke tashi kala,kala, Duk wanan kamshin anayin shi a kan maigidan da zaidawo yau daga gurin aikin shi can garin Lagos, Tun jiya ya bugo masu waya yana mai sheda masu cewa yau zai iso, sanin da sukayi cewa ysna saman hanya, Yasa su wanan girke girke da kara gyara gida duk da dai gidan nasu ko yau she fes yake,bazakace akwai yara agidan ba, Bayan sun kammala aiyuman su ne sun gyara guri sai kuma,suka shiga gyaran jikin su, Duk da zaman Iliyasu ma,aikacin custom ne hakan bai sa ya wadatar da matar shi da komai ba, Don dai da ka ganta kasan cewa zaman hakkuri takeyi kawai, don babu wani kama na nuna wadata atare da ita, Allah yasa mata hakkuri da dauri sosai don sam baka taba gane halin da take ciki, Cikin wanan halin hakkurin da takeyi bai hana yan uwan mijin ta,sata gaba ba da fitina Don su gani sukeyi ai duk wani bida na Iliyasu yana gurin Anty Dije da yan uwanta, Idan suna wanan zancen bata bata ranta saidai tayi murmushi kawai, Don takan ji dafin rashin gane sirinta da basuyi ba har suke ganin cewa komai na hannunta, Basu san cewa dan uwan su ne mai laifi ba, Harkokin shi kawai yake yi a can bariki abin shi, Maryan zaune tana kwalliya a gaban madubi da ke kuryan dakin anty Dije Wanda har in tana son yin kwalliya mai tsayi dole sai ta shiga har kuryan dakin na anty Dije, Sauri take yi ta tafi karbo ma anty Dije dinkun nan ta a uguwar Rimaye, Waje wata yar uwar maman su Anty Dije din don matar ta iya dinkin zamani sosai, Atamfar code,viore ne mai ruwan makuba da milk, ajikin ta, Dinkin riga da zani ce tai daurin baya ta kulle shi a tsakiyar baya, Turaren Anty Dije tadan fesa kadan , Saida tagama hada komai tadauko dan wani karamin hijabin ta, ta sa sai takalman Bella, da tasa, a kafar ta, Cikin yar muryan nan nata take sallamar Anty Dije a hankali don gudun Issalam kada taji ta tace zata bita, Don ance tayi sauri ta dawo, dawuri saboda kila dasu anty zatayi amfani A gidan mama Asabe tasa mu bata karasa hada dinkin ba don haka tabukaci mama Asabe ta bugawa Anty Dije ways ta sanar mata cewa da dan saura kadan kafin a karasa, Tana zaune tana jiran dinkin saiga wata budurwa yar gayu ta shigo gidan Daganin yadda sukeyi da mama Asabe kasan sun saba sosai, Inda maryam take zaune budurwar takalla tace ma mama Asabe Asabe ina kika samo wanan yar budurwan mai kyauwo haka, Saida mama Asabe tadan kalli gefen da maryan take zaune tana mai ci gaba da dinkinta tace, Diya tace, tazo karban dinkin su ne Kanyan anty da ake dinkawa tadan taba sanan ta kai zaune saman kujerar roba fara dake dakin da mama Asaben take dinki a ciki, Turamay zani tafitar guda biyu masu ba,lain kyau daga cikin bakar ledar da tashigo da shi a hannu, Kai inji mama Asabe amma dai wanan zanin akwai kyau wallahi kamar su sukayi kan su, Budurwan tana wani ya mutse fuska tace niko kinga Asabe zanin bai suyi min kyau ba Kodon bani kawai akayi shiyasa ban ga kyaun shi ba, Mama tana dinki ta ce kedai yar rainin wayo ce taya za,a baki abu kice kin raina, Amina halinki sai ke wallahi, Ai ma, mutum abin arziki irin wanan zukakan zanuwar haka ki ce wai ke basuyi maki ba, Gyalen da ta yafa ta kwabe, ta koma, daga ita sai wata yar rigar t,shirt ajikin ta, Ta mike ta bude fridge din mama Asabe ta dauko roban ruwan Goje water tadan fara kwakwada, Maryam dake zaune gefe tana mamaki da kallon ikon Allah, A, ranta tace wanan duk cikin wayewa ne haka kuma, Ka cire hijab a gidan mutane, idan maigidan yafado fa ya zatayi, Muryan Amina yadawo da ita daga tunanen da takeyi Amina ke cewa mama Asabe bayan ta gama shan ruwan da tadauko a fridge, Tsaraban Aisha ne fa Aisha mama Asabe, ta tambaya da mamaki, Ita fa inji Amina kinsan ta da,kwashe kwashe, wani dan Arne ta samu yake kashe mata kudi haka, Arne fa inji mama Asabe mai dinki, Amina tace wallahi ke dai, Niko bayerabe ne musullumi ai ban iya zama da shi balle iyamuri kirsta, Mama Asabe tace ke ko indai musullumi ne ai ba matsala, tunda Allah bai hana aure a tsakani ba Amma ace kirsta gaskiya abin baiyi ba, Amina tai wani irin turo baki tana mai daga kafada da watsar da hannayen ta alamar nuna oho ba ruwan ta, Mama Asabe tace amma dai Amina nagane zancen ki har da kushi a ciki Nan gardama ya kaule masu tsakanin ita da mama Asabe Daidai lokacin da mama tagama hada dinki tana kokarin nikewa tasa a cikin leda ta miko ma maryan, din, Tamike tana mai ce madu sai anjimar ku, mama tace ku rage min tsarabar Lagos in ankawo maku Dariya maryam tayi kawai ta ce to mama zan fada mata in naje, Ganin motar Ya Iliyasu a kofar gida ya tabbatar mata da isowan shi, gari, Cikin nuna farin ciki da jin dadi ya iso duk daxtasan cewa ba wai wani abu zaizo masu da shi na marmari ba, Amma dai tana murna Allah yakawo masu shi lafiya Yana zaune saman kujera rungumay da yaran shi ta shigo dan matsakaicin falon nasu, Har kasata kai tana mai sannu da zuwa yai yar dariya yace little mummy ance min an aike ki , Tai mai anzo lafiya da murnan ta shima a cikin fara,a yake ansa mata, Iyalin iliyasu sun cewa ko ba komai indai har yana gari suna cikin farin ciki a ko yaushe Don gidan su yacika da baki masu zuwa da yan bukatun su akai akai, Kasan cewar zukatan mutane ya mutu yanzu don ba,a maida roko bakin komai ba, Sai kaga mutum magidanci bai aikin komai sai bin gida,jen masu dan abin hannu ana rokon su, na cefane, Yau kwansn iliyasu biyu da dawo wagarin don kusan sati guda yake yi idan ya zo garin, Zaune suke suna hira shida Anty Dije bayan fitan wasu mata yan uwan shi da suka shigo Wani almajiri ne yai, sallama a kofar gida ya ce ana kiran Assalam wai a waje , Daga Anty Dije har mai gidan ta, saida suka kara tambaya cikin mamaki, Maryan wace ke kitchen tana kokarin gyara kitchen din Zuwa tayi tadan leka don taga kowaye ya aiko kiran Assalam haka, Tsaye suke jingine da wata mota mai kamar ruwan kakin soja, Dan lekawa,tayi kadan daidai yadda basu ganinta tadawo cikin sauri , A,kofar shiga falo ta hadu da ya iliyasu, da ke kokarin fita waje don yadiba, Duk kan su maryam suke kallo don jin ko waye a wajen, Inda Anty Dije take tsaye ta nufa tace cikin murya kasakasa wanan mutumin ne fa wanda Assalam yake lakewa, Iliyasu da ke tsaye ke tambayar maryam waye ne a wajen wai, Murya cikin taushi anty Dije tace wanan abokin jibrin din gidan baba bala dana fadama, Kasancewa duk wani abu mai muhinmanci sai anty ta fadawa mijn ta don gudun zargi, Dan shiru yayi can kuma sai yakama hanyar wajen Basufi minti koda uku ba sai gasu sun shigo cikin gidan duk kan su, Shi maigidan shi ne gaba, sai su biyu a bayan shi,, Ya iliyasu nacewa jibrin nadauka ma ko wani bako ne da naga ka tsaya a waje kana cewa wai akira ma Assalam, Bayan sun zauna a falo ne suka dan taba hira a tsakanin su inda aka gabatar masu da abinci, Duk da Joseph baiso cin abincin ba am a saida ya illiyasu yasa shi ci Sannu sanu daga hiran su yafara sake jiki har zuwa lojacin da Assalam suka dawo daga gidan kakan nin su, Dagudu Assalam ya fada jikin Joseph yana murna, Batare da yai magana da kowa ba ya mike tsam rike da hannun Assalam zuwa gurin motar shi waje, Sai a lokacin Ya Illiyasu yake tambayan jibrin ko waye Joseph din, Nai yai mai kwatance da mahaifin shi da kuma mahaifiyar, shi, Saidai bai fada mai ko waye Joseph din ba ayanzu Yadai bashi labarin haduwar su da Assalam har yadda jinin su ya hadu, Lokaci guda don yace ma ya illiyasu kusan ko yaushe su kayi waya sai yatambaye shi labarin sturbonboy, Abinda da da mahaifi, duk mai son mutun akace yaso dan shi, Hakan yasa ya illisu jin dadi har a cikin zuciyar shi, Ganin su mukayi Assalam da kaya nike nike sun shigo harda keken yara, Gaba daya muma fito waje muna kallon wanan irin shakuwar Bayan sun aje kayan ne yaya yagaiyace su cin abin cin dare a gidan shi, Joseph din yaso ya doje yaki zuwa saboda yana son ya shiga evening services yau, Amma ba yadda ya iya kawai sai ya amsa gaiyatar yaya din, Saidai su uku suka zo tare da KB akazo wanan karon, Abincin hausawa mukayi yau tuwon shinkafa fara da miyar Alaihu da yakuwa, sai yar kabewa da mukasa da busashen kifi, Mundauka cewa baza suci abincin ba sai gadhi duk an cinye sai kwano kawai, Duk kan su sunyi mamakin ganin anyi girkin mutanen da a gidan matashi kamar ya iliyasu, Saboda sanin da sukayi yanzu kiuyya bai bari mata suyi girki mai kama ciki, da dare, Saidai kawai aima namiji taliya ko indomie da dare ko dafa duka, Saboda kiuyyuya kawai, don kada a motsa jiki, Hira sosai sukeyi yan sungama cin abincin kamar sun dade da sabawa da junar su, Shiko Assalam yana manne a jikin Joseph har yai barci,zuwan wanan lokacin, Ganin haka ya iliyasu yaba Joseph bakin cewa duk lokacin da yazo kuma yana son ganin Assalam yashigo kawai gurin anty Dije, Kuma miyar da yace yana so na hausawa yadinga fada mata ai mai, irin da yake so, Wanan shine silar kara shakuwar yan gidan su Anty Dije da Joseph, ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, Zaune suke a majalisar su,inda suke hira duk marance ( yamma ) akantitin B C G titin da ya mike zuwa kaduna , minna Abuja tare da,wasu yan kauyu kar dake hanyar, Duk marance a nan su KB ke yada zangon su, suyi ta hira ko aita shan matar juna a tsakanin su, Wanan abin ko yaushe yana kara burge Joseph don saman yan yaren su basu da lokacin hakan , Ko yaushe ana cikin kasu ko bakin titi gurin bidan kudi, Yan zun kuma sai dai in har yaso shiga taro saidai ya yaje koda clubs ko kuma wani park ire iren wuraren sheke aya amma ba irin haka ba da hausawa ke yi, Shiyasa shi har gobe yana sha,awar tarbiyan bahaushe, Joseph jin shi yakeyi kamar bai da wani harkan komai a gaban shi, Zuciyar shi na mashi fes a duk lokacin da yake cikin irin wanan yanayin, Wani matashi mai suna sulaiman ne yazo sama wata mashin rober,rober yanata,washe baki, Ya sayo sabuwar abin hawa, sai sam barka kowa ke mai a lokacin saboda ya huta da yawo a kasa ko saman kabukabu, Kowa sai zuwa yakeyi yana duban man shin din cikin kulawa, da yiwa Suleiman fatan alheri, Joseph dake waya a lokacin kuma yana kallon su sai abin ya daure mai kai so sai Don saboda mashin kawai da ko gabadayan su zai iya sai masu wanda ma yafi wanan tsada suke ta ma suleiman murna haka, Sai kawai yaji tausayin su yakara kamashi duk da sunan wai suna aiki gwaunati ke nan amma gashi yar mashin kawai na basu sha,awa, Jesus crisis yace a zuciyar shi don ba karamin sa,a ya taka ba shi da Allah ya maishe shi haka cikin su, Don ai a da duk tare suka taso kuma yan zun ne yasamu wanan ci gabar duk da dai basu san ko shi waye ba to amma dai sun san yana da shi, Muryan Nasir ce tadawo da shi inda yaji Nasir na fadin cewa Allah yasa ko yar Suzuki yasamu ya saye shima, hakadai duk sukayi ta hira a tsakanin su inda kowa ke fadin albarkacin bakin shi, Har zuwa goma na dare suka kai agurin suna hira sannan KB yadauke shi sama wata rubaban mashin din shi zuwa gida, Tun da safe yabar gari ya ko gurin harkokin shi don ci gaban shi,, Tunda yadawo yadawo da kudin tallafawa mutane da dama aran shi, Din shi a ganin shi duk wanda kuka wahala tare har Allah yabaka samu daga cikin ku to bai kamata ka manta da yan uwa ba, Sanar,ar da suka fara shigo da dan yar Gas dama ainihin pure Gas din, Gani harkan ta karbu yasa shi yin kokarin gani sun gyara system din business din yadda ya kamata, Shigowa da mai din kasar arewa yasa shi kawo KB daga cikin wa yanda za,aiwa interview din zama members nan gaba, Waya yai ma KB yace su hadu Abuja next week Wednesday, don su dan tatauna, akai, KB duk da bai sam komaiba bai yi kasa a gwaiwa ba ya shirya zuwa Abuja din, don ansa kiran da joe ya mashi,, Cikin lokaci ya samu isa Abuja inda yasamu, har Joseph ya cika mai duk wani form da ya kamata,. Briefly Joseph yai mai bayani sai gashi kawai, ankira shi don yashi ga ciki duk da bawasu tambayoyi bane masu tsauri amma dai Joseph din yana darrr kada kb ya kasa amsawa duk da baida shakku akan shi, don yasan cewa yana da kokari,, A cikin ikon Allah KB yai nasaran lashe interview din ,,,a cikin masu yi harda Joseph a cikin su, Murna da farin ciki a gurin su baa musalintawa, duk da har yanzu bawai KB ya gamsu da kowace irin aiki bane, Amma dai gani masu taron ya tabbatar mai da ba karamin aiki bane,, Wanan abin ya jawo ma Joseph surutu acin abokan harkan shi, Don sai cewa suke yi ya dauk hausa ya sa acikin harkan shi ya bar yan uwan su sun fadi, Wanan damar a cikin sune ya kamata wani ya samu ba,a cikin northern side ba, Suko hausawan dake cikin su sun yi mamaki kwarai daganin Joseph ya kawao candidate din shi bahaushe, Tun a wurin akaba KB sabuwar mota da kuma gida inda zai dinga besing a Abuja Sai sabuwar office da aka bude masu washegari, Kabiru gani al,amarin yakeyi kamar a mafarki wai yau shine da wanan abin da bai taba tunane samu ba, Sai gashi Allah ya bashi cikin dan lokaci guda, don haka bakaramin nasiha Joseph yai mai ba don ya fada mai cewa sai yasa ido ga harkan so sai kuma ya rike gaskiya don akwai bata gari wa yanda zasu iya batasgi cikin dan lokaci, Don zasu iya hada mai tracks kalakala don kawai ama wani hanya,shi a kore shi, Kwantagora ta dauki zance kwaaaaa cewa KB yadawo da sabuwar mota, ya samu aiki, Amma ba,a san kowace irin aiki bane haka da har ya samu wanan cigaban cikin lokaci guda, Wasu suka fara cewa ai yafara irin harkan Joe ne Joe din ya jefa shu cikin kungiya, Wanan zancen har ya fada a kunen KB da yan uwan shi, Inda mahaifin shi yakira yin mitin tare da duk wani dan uwanshi tare dashi KB din,,,, Anan KB ya fada masu cewa wallahi har ka ce ta sanar man Gas wanda duk wani Gas da zai shigo nan arewa saida sa hannun su a ciki, Nan dai yai masu bayani har suka fahinta suka kuma yi mashi fatan alheri a harkan,,, Saodai cikin gari kan wasu sun yarda wasu ko ba su yarda ba har yanzu,,, Sadiya Mohammad jodi wata sabuwar matashiya ce mai tashen budurci a cikin gari Tun ranan da taga Joseph tare da su Aisha Allah yasa mata son shi a rai saidai kawai matsalar ta da akace mata ba musullumi bane shi, Don har ta kasa boyewa a zuciyar ta saida ta samu jibrin tai mai magana akai, Dayake akwai wasa a tsakanin su yasa Jibrin duk inda ya ganta sai yace mata ta Joseph ita kuma sai tace aa, saidai Yusuf, Wanan wasa ko yaushe jibrin kewa sadiya, indan sun hadu ita ko bata gajiya da bashi ansa kamar kullun, Maryam ce zaune tana wanki a bakin famfo gidan su. Wayan Anty Dije yai kara alamar kira ya shigo mata, a lokacin Maryam tamike cikin tafiyar ta maikama da rangwada kasan cewa ba wani jiki gareta ba, Daukar wayan tayi don ganin bakon noba ke kira, cikin yar siririyar murya tace Assalamu Alaikum, Hello Anty kuna lafiya ya yara da gida, Wayan ta dan daga ta kalla,sai kuma ta kara manna wayar a kunen ta, Wake magana ne tace ? Anty Hadiza nake nema pls aka bada ansa, Bata nan ta,shiga makwabta yanzu, dan shiru yayi sai kuma yace Assalam na kusa pls,? Baya nan shima tare suka tafi, ok in tazo ki fada mata Joseph ya bugo mata, Joseph kuma ? Joseph fa, kai is wrong noba pls Kada ka kara bugowa nobar matar aure ce pls Dan murshi yayi har tana iya jin shi, alokacin yace ba nobar maman Assalam bane? Tsuki tayi tana fadin mukan ina muke da wani arne wai Joseph da zai kira Anty Daidai lokacin da ta gama fadi ta kashe layin, Tana ta faman fada wai kawai don suyi magana da matan mutane suke kiran wrong noba,,, Shiko joseph dake zaune a saman wani leda cushion ya rike wuyan shi da hannu bibiyu ya furzar da iska, daga bakin shi, In akwai abinda yafi mai munin ji shine ace mai arne, ko kafiri,,,, Tun yana yaro yai hating din wana kalman a rayuwan shi, Don in mutane suka ga su jibrin ko kabiru tarrme dashi lokacin sai yaji sun ce baku barin yawo tare da dan kafirai ko ko dan arna ko, Wani bukin Christmas daya kawo masu abinci kamar yadda su ma suke bashi abinci sai cewa wasu mata sukayi Ku fita mu na da abincin kafirai a cikin gida kada muyi amai Wa zai ci abincin arna jagwagwalen banza kawai babu ko tsarki, Shikuma yadai san cewa duk wani tsabta a lokacin mamanshi tanayi, Kuma shi har gobe idan ya kewaya yana tsarki kamar yadda ya ga kowa nayi, Amma sai ake ce mai wai baida tsarki haba mutane ne,???? Anty Dije tana shigowa tare da su Assalam daga makwabta ko daki bata shiga ba,,, Maryam ke fada mata cikin fada cewa wani kafiri ya bugo mata waya wai sunan shi Joseph nikan nace wrong noba ne Dan rainin wayo kawai Anty Dije dake tsaye sororo tana kallon yadda maryam ke ta faman halako fada, Tace kafirin banza kafirin wofi don ma bakiji hausan shi ba wallahi kamar fa hausan mutum kwarai, Anty Dije tace maryam ina fatan duk wanan zancen baki fada a waya ba dai ko, To may ye Anty in ma na fada mai kawai ina aikina kafirin banza ya kirani, ya bata min lokaci, Saida Anty ta zauna take cewa maryam mutumin nan ne fa abokin Assalam,kike ta surfa ma masifa, Barin wankin tayi tana kallon Anty Dije tace Anty ce min fa maishi yayi sunan shi Joseph fa, Shine mana Anty takara ce mata da dan karfi wai anty shi kafiri ne dama ba musulumi ba, Ke baki sani bane dama Hmmmm lalai mishon bat da musulumi, Wallahi anty ni na dauka cewa musullumi ne shi duk ganin da nake msi, Dan guntun kara dake gefe anty tadan duka ta dauko tana cewa wallahi ke dai kamar ace mai musulumi Don dai gaskiya ya duk halin shi na kwarai ne, wallahi, Daga inda maryam take tsaye tace furen juji kenan shi, Ga halin kwarai amma ba alkiblan kwarai, Dama malamin mu na islamiya ya fada muna ce wa akwai irin wa yan nan mutane acikin yan Ahal,kitab, Saidai basu da yawa so sai daga cikin su, masu halin rayuwa irin na mumunai Daga haka ta tabe baki taci gaba da wankinta tana cewa Assalam abokin Christian, shiko sai dariya yake mata don bai san ma,anar maganar ta ba,,, Yinin ranan sai maganar ta dan tsaya mata a rai kawai tausayi yabata mutum kamar wanan ace baya sallah Allah ya kyauta kawai take cewa aranta Sai ma daga karshe takama jin haushin shi, da takaicin kawai,, Mr Emanuel yanzu girma ya fara kama shi don haka yanzu iyakar shi zama gixan man su ya daina yawan harkoki kamar da Kamar su saida manja, saida robobin aiki irin na mata duk suna da shagunar su acikin garin kwantagora, Yau ma kamar kullun zaune yake saman wata far kujera kamar kulun da yamma haka yakeyi sai zuwa shidda yake wuce wa church wani lokaci,, Wani musa mai aski ne yazo inda yake don sun saba da musa,wanzami tun tuni Saboda zaman uguwa guda, da suka taba yi ada, Shine sabon su yai karko har zuwa yan zu Musa yakan dan biyo ya samu dan abin ihisani akai akai Bayan sun gaisa ne yake kokarin zama gefen da Ema mai manja yake, daidai lokacin yake cewa Ashe taimakon da yaron ka yayi wa dan gidan Tanimu kafinta ke nan Mr Ema ya ce taimakon may ke nan fa, acikin hausar su irin ta IBO,,, A, ba ance ya samo mai babban aiki a Abuja ba har ma yai kudi lokaci guda, Wani yar Mr Ema yaji kamar an datsa mai mashe a zuciyar shi, Sai da yai kokarin boye ma musa wanzan da halin da ya shiga tukun sanan yace har ya fara aikin ne ko, Musa wanzan yace kai tun yaushe aiki kan har mun fara cin moritar ta, Don nafito zan wuce kauye nagan shi yana magana da wasu masu aikin gina wai yana son ai masu katangar gidan su,, Wani iri mr Ema yakaraji a ran shi watau ke nan har maishi yadan fara karfi da tai makon Joseph din, Alhalin ga yaran su cikin gari birjit da suka gama karatu suna ta bin shi yasamo masu aikin yi yana cewa ba aiki yanzu,,, Musa na ta zuba shi bai ko jin may yake cewa a lokacin,,, Kai musa pls zan tofi wani anguwa ka tafi kawai zamu hadu gobe ke nan, Daga haka ya tashi sai gurin motar shi ya nufa rai bace Gidan shi ya nufa cikin fada yake kwada ma Samuel kira Ya wurgat da sandar da yake yawan rikawa mai alamar sandar sarauta, Lokacin Samuel yafito daga cikin gida inda yake daka sakwara, Call your brother for me pls, Cikin mamaki Samuel din yace ok Dad, Kira daya na biyu ya dauka JOSEPH da kakausar murya yakira shi hakan yasa Joseph din sani wani muhinmin magana ya faru Don haka yai shirin sauraren baban na shi,, How may time D I warn you about dis hausa boy's,,, ?? Baba what's going on. Sai kuma yace cikin yaren su maya faru baba, Ya akayi ka samo ma yan gidan hausawa aiki bayan nayi ma warnings akan MAKu da su, Sosai yake mai masifa shi dai sauraren shi ya keyi batare da ya ce uffan ba,, Daga karshe kuma sai ya sasauta muryan shi zuwa lalashi, Yace You have to be,careful with dis people they are very dengerous, Haka dai yai ta ma mai nasiha shiko yai shiru kamar mai saurare, A karshe ya sheda mai cewa yana jin kunya abokan shi da yan churches din su su ji cewa yai eanan aikin,,,, ZEEEE. MAKAWA. 👏👏 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Why why mutane suke da gulma haka, may ye aibun taimaka ma KB dayayi da har za,a fada ma Dad din shi, Wai may yasa mutane basu kaunar suga cigaban yan uwan su ne musan man hausawa, Don dai yasan cewa wanan maganar daga bakin hausa yafito zuwa kunen mahaifin shi, Zubur ya mike tsaye daga inda yake daga shi sai dogon wando da singlet a jikin shi, Gurin window dake facin din titin da ke unguwar su ya nufa, Fitinlo ne karara suka haske ko ina sai kuma duhun dare da ya gauraye gari lif, Ya kai wani dan lokaci a gurin tsaye yana kallon sararin samaniya kawai, Daga karshe bayan yasamu mafita yai wani dan ajiyar zuviya mai nauyi, Fridge ya bude alcoholic ke ciki kala kala duk sunyi rabar sanyi yadda yake so, Hannu ya mika da niyar yadauko wani mai berry a ciki, Caka hannu shi ya tsaya daidai wuyar kwalbar Muryan Jibrin ne ke mai yawo a kwakwawa duk addinin mu bai yarda da shan giya ba, Duk wanda ya ganka a lokacin kana cikin maye baya kara kallon ka da dara a idon shi, Don duk sanda ya gan ka wanan yanayin mayen dayagan ka aciko zai fado mai zuciyar shi Kaga kimar ka da mutuncin ka yazube a idon shi, Idan kuma ka samu iyali za,a dinga goranta masu cewa uban su dan giya ne, ai, Cikin sauri kamar wanda akai ma tsawa ya dauke hannun shi saman kwalban, Marfin fridge din ya buga da karfi kamar zai balla ,shi, Da karfi ya fada kan gadon ta baya yana mai rike goshin shi da hannayen ,, A haka wani irin barci mai nauyi ya kwashe shi bai farka ba sai misalin karfe tara saura na safe , Dan hasken ranar da hudu ta cikin labulen window dakin ya haska mai idon shi,,, Mika yayi ya gyara kwanciyar shi don ya cigaba da barci amma sai kuma ya kasa ci gaba da barcin, Mikewa yayi yashiga bayi yai wanka bayan fitowan wanshi ya na daure da towel Yazo bakin gado ya rusun na kan shi saman gado Nan yafara jero addua, our father whose as at heaven , Hello be there name,,,,,,,,,,,,, Bai tsaya ba saida yakai karshen addu,an shi kamar kullun yadda ya saba yi duk safe kafin yafita, Saida ya kintsa tsab ya sauko inda yasamu break fast din shi an shirya mai komai tsab Jin gidan shiru yasa shi daga murya yana kiran Uchee, da karfi, Uchee da ke can yana gyara cikin gida yazo cikin ladabi, Cikin muryan nan tashi mai nuna sanyin hali a koda yaushe yace ma Ucheen ya na duk bear dake cikin gidan shi a kwashe su a zubar da su, Jin maganar Ucheen yayi kamar a mafarki cikin sauri yadago kanshi ya kai wa ogan kallo, Joseph da kanshi ke duke yana dan kada ruwan zafin da ya zuba a cup, Batare da ya daga kai ya kalli Uchee ba yace Yes I Mean it,,,, Uchee zuciyar shi fam da farin ciki yasamu gara basa, yau, Duk yawan giyar gidan oga a ce wai ya kwashe ya zubar, Ba bata lokaci ya kwaso su jiki na rawa yafita dasu gidan,, Saidai a kasan zuciyan shi yana mamakin ko may yasa ogan nashi ya ce ya fita mai da su gaba daya,, KB ne ya kira Joseph din wanda duk yinin yau bai fita ko ina ba yana zaune a cikin gidan shi da ke cikin birnin Lagos,,, Cikin kasala yadauki wayar don bai son yin wani dogon motsi yau, Hello, KB ya kake ne yau ya, Abuja,? Yace a lokaci guda sai KB ya amsa mai da cewa lafiya kalau gashi ma zai tafi suleja dibo wasu motocin da suka samu matsala, Kuma suna dauke da mai a cikin su, Duk da Joseph din yai kokari wurin bashi amsa sama sama, Hakan bai hana KB gane cewa Joseph din yana cikin wani irin yanayi yau din, What's wrong with u, today,,,? KB ke tambayar shi a karshen maganar su da Joseph din, Nothing ma,, Inji Joseph din yaba KB amsa a takaice, kawai, daga haka suka kashe wayan, KB din ne yadan shiga tunane don saboda dan zaman da sukayi da Joseph yakai kowa na iya gane mood din wanin su,,, Duk abinda KB keyi hankalin shi na gurin Joseph don shi a zaton shi ko baida lafiya ne Don yasan cewa ciwon Joseph kamae fitina ce ga duk na kusa dashi, Saboda irin mutanen da basa ciro ne da wuri ranan da duk zasuyi sai duk wanda ke tare da su hankalinshi ya tashi, A hanyar shi ta komawa cikin garin Abuja yakara kiran wayar Joseph din saidai wanan karon muryan da dan sauki sosai a saman da zu, Ejoma, yarinya ce matashiya yar kabilar IBO mazauna cikin garin kwantagora, Tana zaune tare da yayanta da mijin yayanta wa yanda suka kawo ta garin kwantagora da zama, Tun bayan gama karatun secondary din ta ta shaku da wani yaron hausawa, Dan cikin gari shakuwar su ta samo asaline ta yawan zuwa sayen abu da Aminu Aliyu ke yawan zuwa yi a,shagon su Ejoma Ibire, Har takai sun kulla, soyayya da Aminu din batare da kowa yasani ba, Sai da abokan mijin yayan Ejoma suka gan su tare shine suka fada ma mijin yar nata, Ranan tasha fada har d a duka agurin yayyen nata so sai hakan bai masu ba saida suka fada ma pastor don yai mata preach Duk wanan abin bai raba Ejoma da Aminu ba illa ma kara shakuwar da sukayi so sai , Har ta kai Aminu yai mata alkawarin cewa zai aureta Hakan yasa har ta yarda dashi har suka kai ga kara aikata masha,a a tsakanin su hakan yasa Ejoma ta fara bijirewa yayanta da mijin yar nata, A karshe saiga ciki, shiko Aminu Aliyu yana jin ta ce ciki gare sai yace ai sam bashi yai mata ciki ba, Duk yadda yayanta suka so a sulhuta maganar sam Aminu yaki yarda da zancen cewa ai cikin sane, Hankali duk wani IBO dake zaune ya tashi da jin wanan labarin na zance Ejoma ,, Ganin haka yasa mijin yarta ya koreta gidan nasu yace saidai ta koma can gurin Aminu, Wayan shi yake kokarin ajewa bayan ya gama waya da wani Abokin shi da ke zaune a janhoriyar Benin republic, Inda yake kwadaita mai yadda sana,ar motoci da shimkafar kasar wane ke da riba so sai a harkan,,, Kiran Samuel ce ta hana shi aje wayan dai yai niya, Inda Samuel ke sheda mai cewa mahaifin su yana fama da ciwon kafa sosai duk kwanakin nan, Don har takai ko shago da gidan mai bai iya fita yanzun nan, Hankalin Joseph din ya tashi sosai don yasan yadda yakanyi fama da ciwon kafar na shi Sanadin ciwon kafar ya samo asaline tun wani hatsari da yasa mu a saman mashin, Joseph yakira mahaifin nashi inda yake tambayar shi lafiyan jikin nashi Amma sai Mr Ema din yace mai a meke ,you, no worry my child, Na small problem , I go manager amm,,, Yasan cewa zai shigo kaduna sati mai zuwa don akwai wani wanda yake son gani a kaduna din, Hakan yasa bai cewa mahaifin komai, ba, Musalin biyar na na yamma ya shigo garin kwantagira bayan dan banzan gudun da ya dinga shararawa shi kadai acikin mota, Tun kwanar shiga gidan su yafara ganin abin hawan su duk ya cika kifar gidan su, Hankali shi ya tashi matuka daga ganin taron IBO haka, Hon yayi mai karfi wanda dole suka bude mai get, Da kyat yasamu inda yadan parker motar shi a can gefen cikin gida, Tun bai fito daga cikin motan ba ya hango wata yarinya a tsugune gaban elders nasu, Yana ganin haka ya san cewa wani case sukeyi mai karfi, A hankali ya fito daga ccikin motar saidai ganin mutane a gidan ya hana shi bude bayan motar don ya fitar da tsaraban da yazo da shi,,, Tun daga nesa yake jin yadda yarinyar ke gumza ta na ihu da kuka mai ban tausayi, Tana, mai ba da hakkuri sai kawai yaji wani iri a zuciyar shi Don komadai may tayi yakamata,su yi considering din ta a mace ce fa, Ko kallon su baiti ba ya wuce ta gefen su batare da ya tsaya gaishe su yadda ya saba ba, Wanan ya kalli wanan wancan ya kalli wan can, Su na mamakin shi don basu san shi da halin rashin mutunci ba, Samuel wanda ke labe tunda aka fara case din shine ya ke taron dan uwan shi cikin mutunci, Nan yake washe baki babu ko ga ruwa ya fara labarta ma Joseph cewa Na, Ejoma Ebere one hausa boy givern bele,,, D hausa boy now say no b him do amm, Na yin d elders wan punish har,,, Y ,she, give her self to musulim boy, Me ,I know ask u ooo, Joseph ya ce ma Samuel wanda da har zai ci gaba da zubawa, Roban ruwa yadauko ma kan shi daga cikin fridge din, Ganin cewa Samuel baida niyar kawo mai komai Eanka yafada don ya sauke gajiyar shi, Daga cikin bayin yakre jin karar motocin su da mashunar su suna watsewa Saida ya shirya tsab yafito cikin wasu kananan kaya, Abin mamaki wanan yarinyar Ejoma yagani rakube bayan kujera a falon su, har yanzu tana dan sheshekan kuka, Sai a lokacin yake gaisawa da mahaifin shi wanda ke zaune ya mike kafar dake mai ciwo saman wani tsohon tebur, Joseph y u know greet my people,? Baba me i don't have problem with dem woo,, Waiting dis girl do here Dad ? Yace mai zata zauna har asan yadda za,ayi da ita ne, Don ta je tana bin yaran hausawa ga irin hawalan da wo mata, nan, Wayan Joseph din ce tai kara a lokacin wanda hakan ne yasa shi samun sararin guda daga fadan baban, Motar shi ya shiga ya bar gidan nasu don yasan cewa fadan sai ya kawo kan shi a karshe,,,, Tafiya yake yi kawai don yasan cewa KB bai gari kuma , Don haka zuciyar shi ta raya mai cewa yaje wurin little friend kawai ya ganshi,, Anty Dije ta gama abinci kenan tana ko gyara ko ina na gidan, Daga waje yadan tsaya duk da cewa an bashi umarni akan ya shigo ko yaushe yake bukata,,,, Amma sai yaji cewa bazai iya shiga ciki kai tsaye ba Don haka daga daga,waje kadan yadan tsaya yace Salamu Alaikum don Allah ko Assalam na ciki, Cikin mamaki mai ma Assalam sallama duk suke Shiko Assalam har yagane murya da wani irin ihu yafita kofa inda Joseph ke tsaye yadaga shi sama cak yana dan juya shi, Sai suka kama dariya a tsakanin su, daidai lokacin da duk sauran yan gidan suka leko ta kifar falo suna kallon su, Ànty Dije ke cewa a, Joseph shine baka shigo ba ka tsaya daga nan kana cewa kana ma Assalam sallama, Dan sosai kai yayi da key din motar shi yace ai zan shigo nakira Assalam ne yai min jagora, Falon anty ta bude mai yashigo daidai lokacin da maryam ta dauki buta don zuwa yin alwalar sallah magrib,, Bayan sun gaisa da Anty dije sai kwai ta fara gabatar mai da abincin a lokacin don dama har ta gama komai,,, Cikin nuna jin kunya yace mata ya gode bazai ci ba To ke nan kai kana jin tsoron cin abincin mu Joseph shine shi Assalam, ka ke kawo mai sweet, time to time, No haba Anty gaskiya ba hakana bane, Kawai dai naga cewa nashigo late evening ne kin rida kin gama cooking din ki ko Idanzaka ci kaci kawai don sama mu a aje extra ko yaushe, Badon yaso ba yadan dauki spoon ya fara ci a hankali, Yamai yar jin nauyi da kunya duk da cewa daga shi sai Assalam ne a falon zaune, ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Ejoma ce zaune a saman wani dutse dake ta, bayan dakunar kwanan su zaune, Duk abin duniya yakai mata ko ina sai tunane take yi lokacin da Amina ke mata kalamai masu ratsa jiki Har yake mata tayin shiga cikin addinin su yana cewa zai aure ta zai zamay mata tamkar uwa ko uba, Dan siririn hawaye ne ya silalo mata daga cikin idon ta ya biyo ta kumatun ta, Muryan Aminu ke mata yawo a kwakwalwal ta inda yake cewa bai taba ganin wata mace mai irin surar jikin ta da yaji yana so ba aduniyar nan in har zata amince mai shi yayi alkawarin aurenta, Wa yan nan kalaman ne sukayisukayi tasiri a zuciyar Ejoma har ta yarda da maganganun Amina yai galaba akanta, Don Alokacin tana ganin kamar cewa tafi ko wata mace dace, da masoyi, Kamshin turaren shi na THE wanda ya hade dana JOJOBA, Shiya dawo da ita daga tunanen nadamar da takeyi a lokacin, Kamar ya wuce inda zai tafi amma kuma sai yanan yarinyar da irin yadda yaganta zaune a takure yasa shi jin wani irin tausayin ta alokaci,guda ya tsargu mai a zuciya, Cikin yaren su na IBO yake mata magana, a cin taushin harshe, Yake mai ce mata may ke faruwa da itane har hakan yafaru da ita, Wani sabon hawaye tafara shirin sakowa saida ya dakar ta da ita, Cikin daga mata hannu yace Hy ,I don't want dis your cry, cry pls,,, Just tell me what happen with u, Nan takoro mai da duk abinda yafaru tunda ga farko, tana fadi cikin sheshekar kuka, Yana tsaye hannu cikin Aljihu yana saye da farar suit, sai bakin wando, Wata yar jar ,T-shirt ke ta cikin rigar suit din nashi, Ya kafa farin glass a idon shi wando ,zaka iya ganin fararen idon shi kar daga cikin glass din, Yakai wani dan lokaci a tsaye yana nazarin yarin wace duk taba shi tausayi, Don yasan cewa wanan abin yana daga cikin destiny' din ta ne dama, Bayan dan tunanen daya yi na yan dakikoki, sai ya dan nisa kadan wanda ko ita ba lalai ne in har taji ba, Nobar wayan Aminu yabukata daga gurin ta, ba, bata lokaci ta bashi dama nobar na a kanta ta haddace shi tsab, Tana mika mai bai tsaya ba ya juya kawai ya wuce abin shi, batare da yace ma mata komai ba, Tuki yakeyi amma zuciyar shi jin ta yakeyi kamar zata fito daga cikin jikin shi, Why some people are not trusted, Why men's are cheating girls nowadays, Some say girls are to blem too, Amma shi a gurin shi ai mace abin tausayi ne sosai,, Amma wasu maza sun dauki mace abin wulakantawar su duk lokacin da suka gama da ita, Sosai maganar Ejoma ya tsaya mai a rai gashi ta bijirewa iyayen ta, Shikuma saurayin yayi rejecting din ta at last, su kuma yan uwan ta mai makon suyi hakkuri da ita,sun ki sun dauko ta sun kawo ta nan ,, Unguwar su jibrin ya nufa don KB baya,gari yana Abuja, A wayar shi yakira,jibrin din yana maisheda mai cewa yana son su hadu,, Inda yake yai mai kwatance gurin wani aikin hannu da yake koyo, Joseph saida suka,sha kwana sundan yi tafiya kadan batare da ya waigo inda,jibrin yake ba ya ce, Ko kasan Aminu Aliyu masuga, Jibrin wanda tun shigar shi motar baiyi magana ba ya sai yanzu, Yace dangida namasuga, ke nan ko don naji kace namasuga wanda ke uguwar jankidi,, ko ? Joseph wanda yakai iyakar kaduwa yace ban san ko a ina yake ba, Yana mai karya kwanar filin kwallo yake ce ma jibrin ina son ganin shi ne, Ok kawai jibrin ya ce mai da yace hakana, Nokia shi ya ciro cikin aljihun shi ya kira wani kanin shi Abdullahi, Yake tambayar shi ko yasan inda Abdullahi yake zama, Gurin da Abdullahi yai masu kwatance suka tafi, Aminu yana zaune saman mashin din shi lipan wani abokin shi yana tsaye suna magana ya ji ana mai horn da mota abayan shi,,, Abokin ne ke ce mai ga wata hadadiyar mota fa kamar suna magana nake ga,, Aminu wanda ya juya bayan shi sai gefen shi kawai mutum zai iya hangowa,, Jibrin ne ya isa inda su Aminu suke yai masu, sallama, nan yake sheda ma Aminu cewa,, suna son ganin shi pls, Bayan Aminu ya saurari duk abinda jibrin ya tambaye shi ne, Ba musu ya ce masu lalai yana tare da Ejoma sai dai ai ba wai lalai dole bane ace shi kadai ke taraiyya da ita, Maganar shi taba Joseph mamaki, duk bayanin da suke yi bai yi magana ba sai kallon su kawai yake yi, Daga karshe Aminu ya dan bugi kafadar jibrin yana cewa,, Haba jibrin may zanyi da kafira ina zan kaita, kai min adalci mana kaima,. Kasan cewa ba abinda zanyi da arniya kamar Ejoma a gidan mu, Jibrin Joseph yace cikin wata irin murya mai nuna gajiya da sauraron magana, Muje kawai dan Allah, is ok hakana, Ido yabi su dashi har suka bace mai dagani, Inda abokin shi yake ya koma yana tsuki yace ji mun wa yan nan fa wai akan zancen Ejoma Ebere ne suka zo suna bata min lokaci, Ina ni ina KAFIRA ,,, ARNIYAR banza, wace ko kama ruwa batayi, Dariya mai karfi abokin shi ya shiga yi don jin kalaman Aminu, May kake ma dariya haka ne wai Nuna shi da yatsa yayi cikin dariyar yace bata kama ruwa kai sai yanzu ka san da haka bata kama ruwa, Lokacin da kake holewa da ita duk wanan baizo ma arai ba sai yanzu, Malam kawai kayi JAHADI mukan mu je Onitsha musha bukin gaban dodon tsafi, Kai dan Allah shere kawai da banzaye kaji ni duk in rasa wace zan aura sai ARNIYA Kaifa mutumi dafa cewa kayi zaka musuluntar da ita ka aure ta to yanzu ina zancen musuluntar ya tafi, Kai jafar ka ga alamar musulunta a,wanan yarin balle har kai zancen yinta, Jafar yace gaskiya tunda tana,son ka musuluntar ta ba wani abubane mai wuya, Kai malam kaga idar har kana ra,ayi zaka iya,don wanan ai taimako ne,,, Ka jin tsoron Allah Aminu, Kamar yadda baka so a diyar ka ko wata yar uwanka wallahi su ma haka ne wanan abin yake da zafi a gurin su, Kamar ace kaunar ka ko diyar ka ta hada connection da Dan ,Ahalkitabi, ya zakaji a zuciyar ka, Har kuma ace ya bata ma yar uwar ka, ko diyan ka,, shin zaka ji zafin abin da yai ma ko kuwa,??? Duk wanda yan dake, gurin su kace gaskiya da ciyo wanan abin hakan bai kamata ba, Zafin maganar su ya ji don haka ya hau mashin din shi, ya,buga ya bar gurin cikin fushi,,,, Da hannu guda yake tukin motar hannu shi guda yana yi yana shafan fuskan shi a hankali, Wata bangararen zuciyar shi kuma maganar Aminu ce ke mai yawo a kai,,, Tsawon lokaci suka dauka yana tafiya a hankali da motar, Ba, wanda yai ma wani magana tunda suka fara tafiya,daga shi har Jibrin din,,, Gidan Anty Dije kawai zuciyar shi taraya mai yatafi alokacin,, Kofar gidan Anty Dije yai parking jibrin baiyi mamakin hakan ba don yasan cewa yakanzo gidan, Sai a lokacin ya dan kalli jibrin din yace mai, ina son in,gaida sune,,,, Bayan shigar su cikin gidan sun samu Anty da yara a falo suna karatun hadda, Nan suka zauna suna kallon yadda anty ke wa yaran karatu cikin fasaha,,,,, Joseph yana zaune gefe duk sai yaji yaran sun kara birge shi,,, Saida suka gama ne Anty Dije ta waigo inda suke suka fara gaisawa, Nan sukan dan fara hiran karatun yarw sai kuma na yanayi dake zuwa,,,,,, saidai hiran duk akan zafin da aka fara ne a lokacin, Maryam maryam Anty Dije ce ke kwalawa maryam kira a wanan lokacin Maryam wace ke daki tana gyarawa ta ansa daga can,,,,,, Daidai kuma lokacin da wayar da ke a cikin aljihun rigarJoseph tai kara, Aisha ya kike, ?maryam wace ke shigowa don amsa kiran Anty Dije Idon shi, a lumshe yake magana yadafe goshin shi, Batare da ta kalle su ba tace Anty gani Baki gaida mutane ne maryam , ? Wai may yasa baki iya gaida mutane, maryam, sai a lokacin ya bude idon shi da suke a lumshe, Ya sauke su ga wace ta shigo falon Cikin kwantar da murya kamar ta shagwaba, ta dan rusun na tace ina wunin ku, a kunya ce, Jibrin ne ya amsa mata da lafiya lau, Jin gudan bai amsa mata ba yasa tadan saci kallon shi inda yake zaune, Dammmm gaban ta yafadi don gani wanan dan Christian din da tagani kuma gashi da shiga kamar ta yan musulumai, Shiko ido yazuba mata kamar itace yake kallo, hakan yasa ta wani daure fuskanta ta ma,u,, Don ita dai gaskiya bata ga abinda zaisa su anty su kama hurda dashi ba, Sai muryan Anty Dije ya bugi kunnenta tacewa maryam dauko ma su abin sha dan Allah, In har ba kunnenta ke mata karaba da,zata shigo kamar Aisha taji yace, Amma kuma sai gashi taji yana kamar magana da maishi ta tsigar soyayya, Tir tayi da Allah waddai da irin halin wasu diyan musullumai masu kokarin watsar da daranjan su da kima, soboda kwadai, suna, hurda da diyan kafirai, Ruwa da goran kunun aya, tadauko hade da cups sai dai har yanzu wayar yake yi, Ji tayi yana cewa ina gidan Anty yanzu haka, Cikin wani irin mamaki ta kalli inda yake zaune, yadan kwanta Abayan makarin kujerar, A cikin zuciyan ta tace ji wai Anty Allah ya tsari anty da zama antyn ka, Kwantacen gidan tajiyana ma wace suke wayar tare, Gaskia bazata iya zuba ma kafiri ruwa ba,don haka ta dan gware ruwan da cups din tafito, Amma tana mamaki jin cewa, wai gidan Antyn shi, sai kace wani dan uwar mu, can Allah dai ya raba mu, Tana tafiya ita kadai har tana tuntube,tana guna,guni, a fili ,,,,, Ba,afi yan mintina ba sukaji sallama Aisha, tana sanye da wasu materials dinkin redemaid, tasa yellow, Da wasu takalma masu tsini a kasan su, rataye da wani handbag na company Gucci,,,, Joseph dake zaune yai mamaki kwarai da ganin Aisha har gidan Anty, don bai taba tsan manin cewa zata biyo shi nan ba, Cikin girmamawa ta gaisa da Anty Dije duk da bawai sanin ta Anty Dije tayi ba ,sun gaisa a mutnce da ita Sai ta juya inda su jibrin suke zaune tana mai kallon su, yar karamar harara ta sakar mai,, Tace ance mun an gan ku,a tudun wada, lokacin Anty Dije ta mike don ta basu guri, Joseph da sai a lokacin ya iya magana tun shigowar Aisha yace, Anty Ina son zamu, wuce ,don ina son zanga Dad dina kafin gobe, Ku bari mana kudanci a binci dan Allah saboda ku na kara yawan shi, Da wata kasalaliyar murya ya ansa a hankali da kinbari wallahi mun gode, Jibrin ne yace kai Man ka tsaya kawai kaci abinci don ko mun tafi ba abincin, zakaci ba acan, Juyawa jibrin yayi yanamai kallon inda Anty Dije take tsaye kusa da kofa ya fara bata, labarin abinda yafaru da Ejoma yarinyar da yanzu haka tana gurin baban Joseph da zama,,,,,,, Dawowa tayi inda ta tashi tana maimata Innalillahi ,cikin tashin hankali, da nuna damuwa, Kai kawai take iya girgiza a lokacin saboda tana mamaki, yadda za,ace diyan muna musullumai suna bibiyar diyan arna suna lalata dasu, Cikin sauri ta kalli inda Aisha take zaune sai wani irin salo takeyi a gaban Joseph, Nan ta kara yin tir da irin masi rayuwa irin na Aisha saboda kwadan duniya ka wulakanta kanka, Don dai shi wanda takeyi kashi baima san cewa tanayi ba don ko kallo ta baiyi ba tunda tashigo, Wanda ma nunawa yayi da bai ji dadin shigowar nataba Ita dai Anty Dije fatan ta koyau she Allah yasa Joseph ya gane hanyar gaskiya, Sai a lokacin maryam tashigo falin cikin shirinta na isalamya, Kallo daya ta watsa masu inda suke gabadayan su, Wata uwar tsana da takaicin ganin su ya rufto cikin zuciyar ta Annurin fusakarta duk yagushe, ta bata rai, tana mai murtuke fuskan ta,tankar taga wani mugun abu, Duk wanda ke falin yaga irin mugun kallon da maryam ke watsa masu a lokacin, Amma sai suka dauka kila halinta ne hakana kawai,,,,,,, Barci yake yi amma kuma yana mafalkin garin da yafi kauna lokacin da yake yaro, Watau garin mahaifiyar shi da yafi kowa kaunar ace za,a tafi wanan garin, Kusan wata biyu kenan ko yaushe yana cikin ganin wanan nahiyar a mafarkin shi ko kuma tunane, Don haka yanasa wa ranshi son zuwa ya dibo yar tsohuwa mai munhinmanci tilo guda data rage masu, Watau mahaifiyar maman su wacr tun suna yara aka hana su zuwa gurin ta cewa wai ita witch ce Inji dangin uban su, haka yasa busu saba da ita ba sam,,, Yadda yaso shine sai yaga yadda zancen Ejoma ya kai karshe sannan zai koma Lagos, gurin sanar shi, Amma sai elders sukace sai nan da karshen wata zasu kara zaunawa, Don haka yabata gudu taboye yadda zata iya taimakawa rayuwar da abin bukata,,,,,, Gari ya nuna alamar hadari kamar ,ruwan sama, zai iya fadowa kowani lokaci, Zaune take da dauri zani a gaba duk da tana da riga a jikinta amma daurin gaba tayi,,, Wake take tsinta a wani tire maidan fadi, sai wakan su na yan church take rewa cikin wata murya maiban tausayi, Cikin sauri take aikin duk da ta tsufa, saboda yanayi, da garin ke ciki don ruwa na iya zubowa ako wani lokaci Wani kare ne kwance gefen benci da take zaune, daganin shi zaka ce ko shi kadai ake kiwo a gidan saboda koshi, Jin karan motar da karen yayi yana nufo gidan su shi yasa shi mikewa tsaye yana haushi cikin karfi,kamar zai tashi sama, Horn din mota ce duk ya ruda gidan yar tsohowar dake zaune a lokacin tana kokarin mikewa don jin yadda karen ta ke ta haushi alokacin, guda. Jin horn din mota ya tabbatar mata da cewa a,kofan gidan ta ake horn, din Sam bata kawo cewa bakon ta bane don rabon da ta, ga wani yazo gurin ta har ta manta, lokaci, Don tun lokacin da diyar take zuwa da mijinta dayaran su idan sun zo daga Arewa, Bayan fitinar da akayi ita da dangin mijin yarta yasa duk suka dauke kafar su da ita, Duk da tasan cewa ita ba muguwa bace sheri ne kawi irin tasu, A hankali ta dan fito daga can ta bayan gidanta inda take girki don taga ko waye a vidan ta, Duk da girman da yayi da kuma nuna cewa yana cikin daula, Hakan bai hanata gane jikan nata ba,, a lokacin don rabonta dashi yanzu kusan shekara ashirin ke nan,,,, ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Daga karshe hukuncin da aka yankewa Ejoma baima Joseph dadi ba, Don Samuel ne yakira shi ta waya kamar yadda yabar mai maganar cewa ya kirashi ya sanar dashi duk yadda akayi, Don haka yai kokarin samun nobar ta yace ta shigo motan da zai kawo ta Lagos,,,, Wanan shine silar zaman Ejoma a Lagos cikin karkashin kulawan Joseph,, Yadauki lokaci mai tsawo bai,shigo garin kwantagora, Don har takai mutane sun fara maganan rashi shigowar shi , Saboda kawo yanzu angane amfaninshi a cikin al,uma, duk da zaman shi furen juji bai hana mutane kai koken su gurin shi ba, Shirin kwanciya yake yi dai lokacin wayar shi tai kara, Mika hannu yayi ya dauko wayar daga saman sidedrower, din shi, KB yagani barobaro a screen din wayar yar murmushi yayi don ganin mai kiran nashi a daidai wanan lokacin,, Yadai man inji Joseph yace wa KB Kayi wuyan gani fa mutumina, shiru haka muna ta cigiyan ka a kasar Dariyarn nan tashi ta kasaita yayi da KB yafadi haka na, Yana dariya yana shafar sumar kanshi da ya kwanta mai lun har zuwa fuska, Yace ai lamari ne na rayuwa sai a hankali, yanzu haka tun tree weeks ago olf man ke ta kirana, wai yaji ni shiru, But ina son inyi kokari in shigo, uffer week, don akwai yan aiyukan da zanyi ma Dad, Dariya KB yayi a bangaren shi yace ai ban zata zaka iya kai wa har dis time baka shigo ba kodon mutumiyar don tana ta bugo min waya wai bata samun ka, I beg forget about her ni don old man da mutanen arzikina zan shiga, Wai ya labarin jibrin ne mun kwana biyu ba muyi waya ba da shi, KB ya ce bari kawai man ai old man din jibrin yasamu problem wallahi don ya biya kudin zuwa saudiya amma an cinye kudin case din har minna, Wanan dalili har saida tsohon yai ciwo sosai haka yasa su jibrin cikin wani irin tashi hankali, Wani iri Joseph yaji a zuciyar shi da kyat ya iya furta wa a hankali may yasa mutane suke hakane wai, Mutumin nan ysi iya kojarin sa ya hada kudin shi sai cikin dan lokaci ku kwace, KB yace wallah ma noman wake yayi dis year sosai , Sai yahada da saida dabbobin shi shine yabiya masu su uku shida matan shi, Kaikaikai, haba dai gaskiya akwai tausayi wanan abin, Kawai dai bari za muyi waya da jibrin din in masa jaje, Da,wanan zancen ya kwana a zuciyar shi yana mamakin irin tsoron Allah da mutane basu da shi yanzu, sam Tunda safe ya bidi layin Jibrin inda yake fada mai cewa KB ke fada mai abinda yasamu mahaifin shi, Nan jibrin yakara mai bayanin duk halin da ake ciki tun farko, Wai kudin harda yawa ne Joseph ke tambaya, Jibrin din, A,kaiko akwai yawa ma,na har fa mutun uku ne, Nan dai jibrin ke mai bayanin yadda kudin yake da kuma yadda ake komai, A haka sukayi sallama bayan sun dan taba hiran yau she rabo a gana,,, Tukun mota yakeyi don zuwa depot, yadibo wasu motocin su,,, Amma azuciyar shi yana tunane cewa a she ma bawasu kudine masu yawa na ake biya, Shine har zakaga wasu musulumai gasu da halin zuwa amma sai su tsaya tara duniya, Basu damuwa da kokarin zuwa sauke faralin da aka sa masu, Yanzu diba fa wanan mutumin noma yayi da karfin shi ya biya kudi don kawai yatafi ya sauke farali, Amma aka samu marasa imani su ka yaudare shi saboda , tsaban damfara da yaudara, wanda yasamu ta rashin imani, Wanan zancen yasa shi yin tuna nen cewa ya kamata yakai kakanshi tayi ziyara a Jerusalem, Haka kawai ya tsinci kanshi da nishadin jin dadin wanan tunanen, da yayi Don haka bai tsaya wani bata lokaci ba yafara masu shiri tafiya ita da shi, Don haka ya yanke shawaran sheda ma maifinshi wanan zancen Zaune Mr Ema yake a kofar gidan shi kasan cewa yau lahadi bai zuwa ko ina, Ganin mai kiran nashi yasa shi jin zuciyar shi tayi mai fari kal, Don dai yasan cewa Joseph na matukar kokarin shi wajen kulawa da shi, Bakamar sauran yaran kabilar su da da,zaran yaro ya girma yafara cin gashi kanshi, yadaina yawan kula iyayye ke nan, Ajiyan zuciya yasake daidai lokacin da yake daukar wayan, ya ce Hello Son how are u, ???,,,,,, Shi din ma Joseph din ajiyar zuciya yayi mai kara yace mai, l,am fine Dad, Yace ina ta kokarin kiran layin M,T N dinka baya shiga shine nace barin kira layin Airtel, dinka ko zai tafi, Daddy din murmushi yayi yace ai matsalar services ne kawai, Ya kuke can ya aiki inji Mr EMA, yana tambayar dan nashi, Joseph din yace everything is fine Dad, Mr EMA yace God bless you my child,, Amen yace da murya mai yar karfi, Dan shiru ya biyo baya, sai Joseph din ne yadan kauda shirun da cewa Dad dama ina son shedama cewa zamu tafi Jerusalem ni da Grandma, Which Grandma,? My mother mother, What Mr Ema ya fadi da karfi kamar wanda yaji tsoron hakan, Kana cikin hankalinka yaushe har ka fara hurda da ita, Idan ma baka fara ba bana son kafara saboda kasan cewa is weaked worman, Don ana suspect din cewa itace ta kashe mamanku, Yayi yar murmushi har uban najin shi yace bazata yi komai dashi ba ai Don shi gaskiya bai yarda da zancen da akeyi a kanta ba, Fada sosai Mr Ema ya,dinga yiwa Joseph akan cewa ya janye tafiyar da ya shirya yi shida ita, Har sukayi sallama yana mai jaddada ma dan nashi cewa yafita harkan kakan shi ,,,, Kwana biyu da yin wayar yana cikin damuwa sosai Idan kagan shi basai an fada maka cewa bai ciki dafin rai ba, Don haka yaje gurin wane father, yai mai bayani Inda father din yace mai aida ita muguwa ce bazata tafi wan wurin ba, Sai a lokacin hankalin shi ya kara kwantawa da kakar tashi wace yan uwan mahaifin shi suka azama kahon zuka wai muguwa ce, Tabbas yaji dadin zancen wqnan pastor din don ko ba komai wanan tagiyan zai wanke zargin da ake wa matar, Don haka saida yaga komai ya kammala yakama hanyar zuwa Niger state of Nigeria, Ya iso cikin dare don haka gidan su Anty Dije ya nufa don ya kai mata tsaraba,, duk da yana jin yunwa, sosai, Gashi yanzu in dai yana kwantagora sai abincin gidan Anty Dije yake iyaci, Saboda kawai yardan da yayi da matar don daidai da rana daya bata taba nuna mai kyama ba kamar yadda ya fahinci cewa sauran musullumai nayi mai dan kyan kyami, A falon gidan ya samay su gaba daya suna kallon season film na india, Cikin murna da dauki duk wanda ke falon ya tare shi, banda maryam wace ke kwance saman dogon kujera tana, kallo, alokacin, Anty Dije tace Oyoyo da bakin dare, haka shine baka fada muna cewa kana hanya ba Joseph, Yai yar dariya yace tafiyan haka tazo min wlh Anty, kawai yau naji ina son shigowa kwantagora ne, Bayan sun gaisa Assalam yana makale ajikin shi tun shigowar shi, Yadan kalli Anty yace a tura yara su kwaso maku kaya a buth ko , Inda maryam take kwance Anty ta kalla tace Maryam tashi mana kitafi ku kwaso, A cikin zoboro baki tai kicin da fuskanta, tace a shagwabe sannu, Batare da tajira ansawar shi ba ta wuce tana kokarin daura dan kwalin ta, akai, Har takai kusan kofa tace a bude buth din yake ne, ? Key kawai ya miko mata batare da yai magana ba don ko banza dama shl tsarda magana gare shi, Tayi gaba tana turo baki gaba tana zumbure zumbure, Har takai bakin kofa sai Anty Dije tace idan fa baki iya ba kada kimai barna, Maryam, Wuce wa kaiwai tayi don takaicin da take ji, Kayane shake ga buth irin tsarabar kasar kurmi yakawo masu, Maryan tunda ta samu da taimakon yaran shiya aka gama kwasan kayan Ko kara juyowa hanyar falon batayi ba kawai tashi ge ciki abin ta, Yadan kai wani lokaci suna hira da anty dije san nan yai mata sallama yatafi, Inda Assalam yasa masu kuka sosai, wai sai ya bishi, Sai bayan tafiyar shi ne Anty Dije takewa Maryam fada akan irin yadda take nunawa Joseph din, Anty Dije tace abinda yasa take janshi ajiki dayan biyu ne, Na farko dai ko Allah zai sa ya gane gaskiya, jin haka saida Maryam tadan daga ido ta kalli Anty din, tace a haka anty, Kiga mutum kasurgumin ARNE haka har kike ganin cewa zai iya tuba, Maryam kina ko da tunane akwai abin da yafi karfin Allah ne Maryam, Kinga kuma na biyu yadda yake ra ayin yaran nan kamar wasu jinin shi, Duk saboda Assalam yazo muna kingako badadi in dinga nu a mai tsana ko kyama a fili To yanzu yaya zaki yi da wanan kayan da yakawo maku, Don dai ni gaskiya bazan iya cin komai na kafiri ba, Anty Dije tarasa abinda zatace wa yar uwan nata, Wace gata yar karama sai shegen akida kamar wata malama, Washe gari tunda safe ya nufi gidan su jibrin don gaida mahaifin jibrin din, Yadda yake zato abin yafi nan don duk dan dattijon yaramay yayi baki,sosai, Sundan dade zaune a dakin baban jibrin din da zaitafi yaba shi dubu hamsi yace ai sai mai lemo, Sam yaki karban kudin saida kyat yakarbi kudin da farko Joseph ya zata ko baison abin hannushi ne, Saida dattijon ya yace mai yarage sunyi yawa yabashi ko kadan ne, Yace baba lemo kawai za ,a sai maka kasha,, Bayan fitar su waje ne Joseph din ke cewa jibrin yanzu may ake ciki akan zancen, Nan dai Jibrin ya sheda mai cewa kotu tace mutumin yabiya shi nan zuwa karshen shekara, Joseph yace har lokacin ba,atafi aikin ba ke nan, Jibrin yace kai haba har wasu na shirin zuwa ma alokacin ,, Kai haba impossible inji Joseph gaskiya asan yadda za,ayi musamu baba su tagi wanan shekaran, Jibrin yace yaya zamu man tunda duk dan abi da ke ga baba shine ya hada yabiya masu Joseph dake kokarin bude mota yace ma jibrin a ina zamu samu kujerar, ne, Mamaki karara a fuskan jibrin yace kai bafa maganar wasa bane man kudin mutum uku baba ya bita fa, Joseph yace and so what, Indai har zamu samu ai sai su tafi, Murna jibrin zaiyi ko kuma may Saidai kuma a zuciyar shi ya na tunanen in har mahaifin su zai yarda da zuwa makka da kudin Joseph, Don haka ba bata lokaci suka shiga cigiyar kujerar makka Saida kyat suka samu a wani local government kusa da kwantagora magama local government, Saidai an masu karin kudi sosai akai amma haka ya juye madu yabiya, don dai kwai yadda yake jin kada a wuce baban jibrin bai samu zuwa aiki hajji ba kamar yadda ysi niyya,,, Maganar nazuwa gurin baba aikuwa baba yace sam badashi za,ayi awanan aikin ba, Ina zai tafi aikin hajji da kudin kafiri, Da tambaya dakomai malamai sukace ya halatta su tafi tunda shi yaga dama yabasu kudin shi kyauta,, ,,, ZEEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MA KAWA Wanan tafiyan na mahaifan Jibrin da Joseph ya ba kudin zuwa Saudiya ya jawo muhawa sosai a cikin gari, Har takai wa yanda basu san shi ba yanzu sun fara samun labarin shi,,, Dashi akai komai har zuwa rakiyan su airport a Minna inda zasu tashi, zuwa kasa mai tsarki ,, Wanan abin yabawa Joseph mamaki sosai don tun a nan sun fara ibada Daga can ya wuce zuwa Abuja gurin zancen business din da suke so sufara jonawa, Wanan tafiyar tankar tafiyar don jibrin a kayin don itace samuwar aikin jibrin din,,, Anbashi In charge na supplying din duk wani shinkafa da mangyada da za,a shigo dashi daga wata kasa, Zuwa kasar arewa da kewayen ta, kamar su Cameron da Chadi, Niger Bakaramin sa,an samun wanan nasar yayi ba don mutane da dama sunyi ta korafi akai, Wanan abin yaiwa mutane da yawa dadi saboda jibrin mutum ne mai tsimakon nakasa da,shi sosai, Lokacin tafiyan su Joseph da kakar shi yayi kawai sai ji Mr Ema yayi cewa Joseph yafita tare da ita, zuwa Jerusalem,,, Wanan fitar mutane kauyen suka,dinga mamakin cewa tunda ita witch ce yaya zata iya zuwa can wurin bauta, Wanan tafiyar ta daure wa Joseph kai sosai saboda abinda yagani a can ya banbamta da yadda suke gudanar da tasu,addinin a nan,,,,, Saboda sai yaga cewa ai duk kusan al,adun da akeyi acan kamar al,adan musuluman Nigeria ce da sauran duniya, Hatta da alwala indan bakayi ba ba,za,a bari kashiga cikin massallacin ba, Abubuwa da dama yagani a can sai kuma yaga cewa ai har da musulumai daga wasu kasashe suna zuwa yin bauta a cikin wanan masallacin mai tsohon tarihi watau masallacin, BAITI,MUKADIS,,,, Ya dawo gida zuciyar sa fam da tunane kalala, acikin sa, Kakan shi mai suna Ciyoma, tun acan tadinga wani irin kuka na farin ciki tana mai samai albarka, Addu,an gamawa da lafiya da duniya yadinga mai aciki tasako zancen da ake mata zargi dashi tana mai cewa, Tagode Allah da jikanta ya zama abin kwatance a cikin jamar su, har yafidda ita daga zargin mutane, cikin wani irin magana kamar waka, Joseph dake zaune yana kallon ta a cikin dan gurin shan iska da suka tsaya a wani airport, Yana saye da wani katuwar rigar sanyi,a jikin shi yataso daga inda yake zaune tun fara maganar ta, Ya rugumay ta ajikin shi don maganganu da take fadi sun ratsa mai zuciya sosai a lokacin Tunanen mahaifiyar shi wace a yanzu bata da rai ya fara ji dama ace tana da rayuwa ne da yanzu suna tare da ita a wanan gurin, Saboda yasha tayawa mahaifinshi cewa suzo wanan gurin ziyara amma sai Mr Ema din yace bai son abin wahala shi, Wasu hawaye masu dumu suka silalo mai daga ido zuwa kasar fuskan shi, Yanajin mutuwar uwar su kamar yanzu ne abin yafaru mata mai hakkuri da sanin ya kamata Don yana da wayon shi irin yadda mahaifin shi yadinga wahal da ita a lokacin zaman su, Jin hawayen Joseph na diga mata a wuyar ta ya sa yar tsohuwar dagawa daga cikin jikin shi ta dubi fuskan shi, Ta ce Joseph my child don cry pls, Kara rike kakan tashi yayi saboda yadda yake ji a zuciyar shi ba dadi Sun kai wani lokaci a haka sanan nan ya ja ta da kyar zuwa wurin da kayan su yake gefen wasu kujeru da aka tanadar wa matafiya,, Sun iso gida Nigeria cikin farin ciki da walwala a zukatan su saboda, sun tafi inda kowani dan addin Christian ke burin zuwa,,, Ta Abuja suka,sauka don haka yasa wani abokin shi ya kwaso su, daga airport, Zuwa gidan shi da yake sauka a Abuja,indan yazo, Sai da ya huta san nan ya kira KB yana sheda mai cewa sun dawo shi da kakar shi, Kwanan su biyu abokanan shi suna ta zuwa yi mai barka da dawo wa, Tun wanan tafiyar tasu josepy yasa wa ranshi cewa ba,zai kara barin wanan yar tsohuwar kakanshi cikin wahala ba saboda tana bukatar hutu a rayuwar ta yanzu,, Kwantagora suka nufa daga Abuja inda tsohuwa ciyoma bata so hakan ba don dai ita taso ne takoma gida, Don yanzu bata son wani alaka ya hada ta da mahaifin su Joseph tunda ya iya rabata da 'ya'yan diyar ta, Inbadon Allah ya bata jika mai albarka ba wanda yasan darajan ta, Sai bayan tafiyar Joseph Jerusalem ne labari ya iso ga mahaifin shi irin tai makon da yai wa jibrin again, Abinda takai shi har da hawan jinin shi ya tashi mai dama ko yan uwan Ema IBO sun san shi mutum ne wanda baya son taimakawa na kasa dashi, Cikin dare suka isa don tun a hanya sukai waya da Samuel nan Samuel yake sheda mai abinda yafaru A cike da rashin son taimakon da mahaifin shi baison yana yi ya iso fam a zuciyar shi,,, Murna sosai yan uwan shi sukayi daganin kakar su wace tun suna kanana so sai rabon da su ganta Mr Ema yana dawo Church gurin service din dare yai arraba wanan tsohuwar duk shi ba wai wani girmuwar shi tayi ba sosai Nan da nan anurin fuskan shi ta gushe mai sai da kyat ya iya controlling din zuciyar shi,, A nuse Joseph yafito daga dakin shi don zuwa tariyan baban shi, A fusace ya ke karba mai inda yafara mai sababi na rashin bin umurnin shi da Joseph din baiyi, Yace saboda kaga yanzu kana cin gashin kan ka shiyasa ban isa in sa ma doka kabi ba, Kafada min may hujjan ka na taimakawa yaran hausawa kuma musullumai, Joseph har in bazaka daina hurda da wa yan, nan mutanen ba ina warning dinka kadaina shigowa kwantagora pls,,, Joseph wanda kan shi ke duke tunda mahaifin nashi ya fara fada yadago a hankali ya fara magana acikin natsuwar nan tashi yace Dole in taimaka masu baba saboda sun min abinda yafi haka alokacin da nake bukatar hakan, Rai bace Mr Ema yadaga kai cikin mamakin kalamin dan nashi yace, Kana nufin cewa ba,zaka iya rabuwa dasu ba ke nan, Shiru yayi mai wanan karon yana dai sararon shi kawai, Barin falon yayi saboda yasan cewa yanzu wani ,zafi ba ,zai lankwasa Joseph din ba, Aisha tayi farin ciki sosai da jin cewa Joseph yana gari don tun cikin dare ya kirata yake sheda mata cewa ya shigo, Tasan cewa ita kan kakanta ta yanke saka kenan don ba karamin abu take samu gurin shi ba, Duk dai iyakar ta dashi kawai yan wasan ni kuma ba wani mai yawa ba, Sosai ta shirya ma wanan zuwan nashi saboxa gana da yan bukatoci akan shi da yawa, Shiko tunda safe ya fita zuwa wani kauye shida KB don yana gari, Basu dawo ba sai zuwa dare marance,su ka , iso, garin , Bayan yai wanka ya shirya zuwa ganin little friend din shi, Wanda kusan ko yaushe yana tuna yaron haka kawai son Assalam ya shiga zuciyar shi,, Tsaraba sosai yakawo ma Anty Dije da yaranta don gaskya saida Anty ta kasa yin godiya, Ita kanta Anty wasu materials madu kyau da tsada yasako mata ciki tare da dogayen riguna, Issalam tana gama ganin kayan tace ina na little mummy din mu, Da sauri Anty Dije tace mata ai nawa tare da natane zamu raba, Wani inji Maryam dake kokarin bude fridge a lokacin don ta debo kayan miya, Kai ta girgi,za wa Anty tace a nutse na yafe nikan gaskiya ban so,, Issalam tazo har inda take gaban fridge tace kina so mana little mummy bake ki,kace mama tasaya maki anko ba, Hannun yariyar maryam ta hado guri guda tace Issalam nagode ban so nace maki Anty ce tace ke kyale zata karba ai wasa take yi, Cikin mamakin maganar anty dije ta dago kai kalle ta, da niyar magana,sai kuma ta shiru kawai don irin kallon ki shiga taitayin ki da anty tai mata,a lokacin, Assalam ne yace mama don ba,a sayo mata nata bane wai bata so ko,??? Nace maku bana so kawai simply ta fadi a nutse daidai lokacin da take kojarin barin gurin, A hankali yabita da kallon mamaki saboda sai yanzu yafara fanin tsana karara a cikin idon wanan yarinyar, Ya rasa dalilin wanan tsanar da yar karamar yarinyar ke mashi haka,? Bayan tafiyan shi Anty taima Maryam fada sosai har takai maryam din yin kuka don dai ita gaskiya bata ra,ayin wanan mu,amular da su anty keyi da wanan Arnen sam, Washe gari maryam na tsakar gida zaune da farantin shinkafa akan cinyar ta, tana gyaranwa tana raira kira,ar ta, ahankali, Joseph yai sallama suka shigo tare da Aisha Wacce tai kwalliya cikin wasu irin haddadun buje da riga masu kyau, Kallo guda tai masu ta kau da kai gefe guda don bata son kara daga kai, A hankali tace masu bata nan amma tace indan kazo ga abinci a falo, Daga haka bata kara wani zance ba sai kokarin ci gaba da aikin gabanta tayi kawai, Aisha ce cikin magana kamar rada tace wanan yarinyar na lura bata da kirki wallahi, Ji yadda takewa mutane magana wani iri kamar tana jin warin su, Baice mata komai ba asali ma kamar bai jita ba, KB ne yai sallama sosai irin ta musulunci duk da bawai ta sake mai fuska bane amma dai ta karba mai cikin girmamawa da nuna kula, Daga inda take tanajin suna hira akan wani guy wanda cikin su yake saidai yanzu mahaifin shi bai bari yana binsu sosai, Wai yana zuwa aikin a gonar mahaifin shi ko yaushe , Joseph ne ke cewa gaskiya Umar na ban tausayi don ranan da na ganshi bazaka ce yataba rike biro ba arayuwan shi,, KB yace Umar din ai yace zai zo zuwa anjima don yana son ku hadu dashi, Cikin dan lokaci jibrin yai suna a cikin gari wurin yan kasuwa da sauran manyan mutane, Don jibrin mutum ne wanda ya iya business so sai da jama,a, Ga kuma tausayi da sanin ya kamata, akan harkokin shi, Musan man dayake yana kara samun taimako daga gurin ubangidan nashi a asarice, Ta yadda mutane bazasu iyagane cewa business din shi bane, Saidai su dauka na company ne kawai, Joseph ya koma gurin wanan matar abokiyar mahaifiyar shi mai manja, Inda yake sa ana kawo mata kayan masarufi tana sayar wa talkawa cikin sauki,da rahusa, Ta yadda tallaka ba zai yi mugun wahala ba, sosai wurin samun abinci, Tuni sunan su ya fara fice ga al,umma tun mutane suna zargin su har aka gane cewa business ne sukeyi tsantsar ta don ci gaban mutane, Matasa da dama sun samu abin yi yanzu wanda hakan yasa emirate taji dadin zaman Joseph a tare da al,uman su, Wani abin sha,awa kuma shine idan ya samu labarin cewa a unguwa suna samun matsalar ruwa ko wuta sai yasa sai yasa a tona masu famfon burtsatse ko kuma ya sauke masu transformer, Ya sayo motoncin noma birjit ya tura kauyo ka mafi kusa don tallafawa, Dalilin da mutane suka sa mai furen juji ke nan,don dai yanzu yan kwamintin su na chu sunkirashi mitin yafi a kirga amma yaki halarta,, ZEEEE MAKAWA,,,, [2/20, 9:21 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Alhamdullah Allah yakawo yau, maryam sun zana jerabar su ta karshe a girls day secondary school, kwantagora, Fitowar war,ta kofar class din tai wata ajiyar zuciya gami da fesar da watar iska irin na relief din nan, A hankali take tafiya zuwa bagin get don tafiya zuwa gida jitayi an jawo ta, Assamau musa ce classmate din ta mai photo ta nuna mata tana da bukar suyi photo, Fara photon nasu ne wasu yan gidan jodda suka shigo akayi da su Maryam wace kawo yanzu duk ta kagara ta wuce, gida Don ta huta saboda duk kwanakin nan bata samun barci don mathematics ce zasu zana karshe, Gani zasu bata mata lokaci da yawan daukar photona ya sai ta, sa kai kawai zuwa fita daga school compound din, Wata mota tagani tana jiran wata yariyan batai mamakin haka saboda ga abin hawa na birjit a waje suna jiran yan uwansu wasu kuma samarin su, Tabbas in ba karya idon ta ke mata ba wanda tagani bakin motar KB ne, don ko ina zata gane shi yanzu don yawan zuwa gidan su da sukeyi ko yau she muddin suna gari, Kai takar kamar bata gan shi ba sai tafiya takeyi cikin sauri don ta isa gida, Horn takeji a bayanta kamar kada ta waiga fon tasan cewa ba asaman titi take ba ita, Sai ganin motar KB tayi gaban ta ya Parker dan zuge glass din motar yayi yana mai dan lekowa ta window motar, Sai a lokacin tawaiga batare da ta daina tafiya ba, Ta furta a hankali ina wuni,, dan murmushi ya sakar mata ce little mum babu gaisuwa , Dan murmushi tayi wanda ya baiyanar mata da fararen hakora ta da suke a jere ras a cikin dan karamin bakinta, Tace ai na gashe ka ko, ? Yace zo muje mana mu saukeki a hanya , gani wata classmate din ta zaune a bayan motar yasata dan kara yin murmushi tace ku tafi kawai ai zan hau achaba yanzu, Ganin zai kara mata magana yasa ta tsaya badon taso ba don dai kada mutane su samasu ido Don yanzu ba,a raina sa,ido ga dan karamin abu, Tana kutsa kanta a cikin motar wani irin sanyi da kamshin wanda bata iya tantance ko motar ce ko kuma masu motar ke wanan uban kamshin haka, Ga sanyin AC ya hade da kamshi wanda zai iya sa mutum acikin wani yanayi, (A,uzu,bikalamatilllah ,tamattah), tace yayin da take kokarin zama a motar, KB ne ya juyo a hankali yana mai cewa taufa malama ce injin muka dauko, Maryam da sai yanzu bayan ta samu natsuwa, ta sheda ko wace su KB suka fara dauka a motar Wata, fatima Indagi ce yar gidan nufawa asalinsu mutanen garin Bidda ne zama yakawo su kwantagora, Har suka zama yan gari yanzu don sun san kowa kowa yasan yan gidan su, Bawai wani shiri sukeyi ko a school da ita ba don haka ko kallon inda take,Maryam batayi ba, Baka jin komai daga cikin motar sai kida ke tashi ta yadda ko na wajen motar zai iya jin kidar daga waje, Maganar shi yasa maryam gane cewa yana cikin motar wace tun shigowar ta motar kanta na gefen glass tana mai kallon waje, Dammmm sautin da kirjin ta yabayar ke,nan a lokacin da taji muryan shi a motar yana cewa,idan ka sauke su mu wuce uguwar JANKIDI pls, zanje inga Abdulsamad,,, A hankali kwance yake maganar batare da ya kalli cikin motar ba gefen KB din, A,kofar gidan su Maryam, din suka para tsayawa don su sauke ta, Daidai lokacin Assalam yadan fito ta wajen gidà yà na kallon motocin a ke wuce wa Kokari takeyi ta balle murfin motar daidai lokacin da Joseph din ya dan dan,na gurin da duk security din motar suke, A lokacin kuma Maryam ke fadi cikin siririyar murya, Nagode, ta furta a hankali ta yadda ba wai lalai ne wani yaj abinda tace ba, Hannu kawai shima yadan dago mata alamar ba matsala, Da gudu Assalam yazo ya rungumay mata yana oyoyo little mummy, dan jakar hannun ta yake kokarin karba daga hannun ta, Sai a lokacin yai arba da Joseph wanda ke a gaban mota zaune, Sake jakar yayi ya sheka da gudu gurin motar yana washe bakin ganin Joseph din, Juyawa maryam tayi abinta batare da da tasaya koda kallon su ba UNGUWAR JANKIDI, wani unguwane acikin kwantagora, inda wane abokin sanar mahaifin Joseph yake zaune, Emeka ake ce mai ,,,kusan tare sukazo neman kudi agarin, tun suna matasa, Saidai Allah da ikon shi , cikin wani watan Azumi, sai kawai aka wayi gari wurin wani tafsirin marance da ake yi, Emeka ya kawai sai ga Emeka yace yazo ya musulunta ne, A ranan yakarbi musulunci a hannun babban malamin dake wa maza tafsir, a kusa da gidan sarki, Ranan duk wani IBO da ma sauran Christies hankalin su ya tashi sani cewa kowaye Emeka da sukayi, Duk wani hanya dazasubi don suga cewa sufitar dashi a cikin musulunci abin ya faskara garesu, Har kudi suka hada mai uban yawa suka kaimai wai yadawo cikin su amma sam yaki karba, Daga baya da sukaga yaki sai suka fara shawaran yadda zasu cuta mai har ya karaya, yadawo masu, Wuta suka fara sama shagon shi a tsohuwar kasuwa inda shagon ya kone kurmus, Da sukaga baizo wurin su ba sai kuma wani dare suka turo har gida aka sace duk dan abinda yasaura a hannun shi suka gudu, Yan kwamitin su sukazo mzi da makuddan kudi suna mashi tayi akan yadawo cikin su, Amma san Abdullsamad yaki dawowa, yace shi ya shiga kenan, Maimako yan uwa musullumai su tausaya mai su mai tallafi ko wani gudun mawa sai kawai aka shere shi nan, Ganin wahala yai yawa yasa matar shi gudu tabar shi ta koma kasar su, inda takoma ma Christian din ta, Tabarshi nan tare da yaran shi ma,za uku, suna ta buga,buga, Yanzu har takai ko suturan sawa baida shi dan gidan shi rabi ya zube baida kufin gyara saifai kawai Allah ne ke rufa masu asiri su samu abinci, A haka ya auri wata musulma ma sanar saida shinkafa a bakin kasuwa, Yakan je gurin Mr Ema jefi,jefi in abin yadaure mai da yawa, Saidai duk sanda yatafi zai dawo da tarin bakin ciki a zuciyar saboda irin yadda Mr Ema kan ta sake mai maganganu,kuma duk kyautar, da zai mai bawanda zai amfana dashi bane, daga dari biyar tsanani dubu biyu, Rigar shi duk ta yage yage a baya, hakana yake sawa yakoma kamar mahaukaci, ( Allahu Akbar munada wanan raunin wallahi musullumai bamu tallafawa wa yanda suka tuba yanzu,,,,,,,) Mama manja ce ta fadawa Joseph cewa yana bukatar taimako sosai saboda sani da tai ma iyayensu tare a da,can,,, Yai mamakin jin cewa har yanzu Emeka Abdullsamad yana agari batare da yasani ba, A hankali suke gangaro da motar su zuwa cikin unguwar wanda akasari duk tsofafin gina ne a gurin, Zaune suka hango shi saman wani tsohon icce dake kofar gidan shi , Cikin wata tsohuwar rigar atamfa duk ta kode ga farin gashi duk ya dan cika mai fuska, Yana zaune kai dagani kasan cewa yana cikin halin hau ula,i,,, Har suka faka motar su baidago kai ya kalle su ba, Saicewa yakeyi a fili Subbahanallahi, Walhadullahi Allahu,Akbar,, Sallama KB yamai daga inda suke nufo shi ya karba masu tare da daga hannu har saida yakai aya, tukun, Sam bai gane Joseph ba a lokacin saidaga baya bayan ya mika masu hannu sun gaisa, duk da kallon mamakin da yake masu namay yakawo su gurin shi, A fuska yadangane Joseph din cikin yare yai mai kirarin gidan su, Inda Joseph din yadan duka agaban shi yai mai yar gaisuwa irinta al,adansu Abdullsamad yadan bugi kafadar Joseph din alamar ya karba mai gaisuwa,, Joseph yace mai baba kana garin nan shine kashige haka shiru, ,, Murmushi yayi yadan mike ya ciro wata tsohuwa ashirin a aljihun shi yana kokarin zuwa wani shago xuwa sayo masu pure water leda, Cikin sauri Joseph yace mai a,a yabari kawai ,acikin nuna damuwa da kulawa yace ma Joseph kabari in shayar daga kai daga cikin dan abin da nake dashi pls, Yanamai daga hannu alamar ban hakkuri agare shi, Dole badon sun so ba yakarbo masu ledan ruwa, gida biyu yadawo katakata cikin sauri ya mika masu, Sukaiyi mai godiya Joseph wanda ke ji alokacin kamar ya zubar da hawaye don tuna kowaye Emeka, Yace mai ina sauran yaran shi suke, nan yake sheda masu cewa, mutum uku suna nan tare dashi, Saura kuma sunan can garin su tare da maifiyar su, Dan shiru ya biyo baya duk kan su kowa da abinda yake anyanawa acikin zuciyar shi a lokacin, Joseph ne kauda shieun take cewa yaso koda zai samu ganin yaran koda mutum guda ne daga cikin su don yana son suyi wani yar shawara, nobar wayan babban ya basu, wanda uban yace yana koyon sanar Carpenter ne yanzu,,, Kudi yabashi dubu hamsi yace mai nada wani sati zaiga sako in ya koma, Sundanyi hira kadan sannan sukayi sallama, dashi suka barshi, cikin tausayawa da irin halin da yake ciki a yanzu, Ganin wana bawan Allah yasa zuciyar Joseph a cikin wani irin yanayi, wanda ya hanashi sukuni, Kasancewar yau jumma,a ne mutane sai haraman zuwa massalaci sukeyi gungu,gungu mata kuma suna gida sun chaba ado kamar sallah, Gidan Ànty Dije ma ba,abarsu a baya ba don daga manyan har yaran cikin kwalliya suke suma, A,wasu gije har abinci akeyi ta musanman don farincikin da darajan wanan ranan, A wasu giden masu dan hali kuma zakuga ana ta rabawa yara dan abin sadaka wasu da safe wasu kuma sai bayan ansauko daga jumma,a, A lokacin da kowa ke ta haraman zuwa sallah jumma,a daidai lokacin ya shigo gidan na Anty, Wanda a yanzu duk sun saba da irin zuwan shi sun,san cewa inhar yana gari to baida gurin hutu sai guri su Saboda har cikin ranshi yana son yananyi irin na antyy Dije Don mace ce wadda tasan kanta dama duk wani wanda yake tare da ita, Alwala maryan keyi da buta a yar tsakar gidan su inda Assalam ke tsaye wai yana jiran tayi tabashi, Muryan Maryam din ne ke cewa kai Assalam wazai kaika masallacine wai tunda Daddy baya gari Joseph yanuna da hannu shi yace da Uncle zamu tafi ma na, ko uncle,? Yana mai tambayar shi, cikin azama, Yace mai eh Assalam, tare zamu, Maryam wace ke kokarin wanke kafar ta ta waiga da sauri takalli inda Joseph din yake, Muryan Anty Dije ne ke cewa, kai Assalam kabar uncle ya huta pls, kabari har Daddy ya dawo sai ya kaika, Kuka yaron ke kokarin yi alokacin ciki sauri Joseph yace No, bar shi inkaishi mana anty, Buta yaron yadauka yafara alwala kamar yadda manya keyi, Ba abinda ya fadowa Joseph a rai sai zuwan su jereselem, da kakar shi, Inda sai kayi kusan duk wasu abu da musullumai keyi na ibada, Gashi Assalam karamin yaro wai har yasan cewa zai gana da ubangiji yayi tsarki, Muryam Assalam ce takatse shi yana cewa nagama uncle, mutafi, Ga mamakin kowa mikewa Joseph din yayi yakama hannun yaro A hanya yaga wasu idon sani yafarka motanisa yabasu yaron yace suje dashi Ana tasowa suka kawo mai shi yatada mota yajuyo tun ba,a tashi ba, Kayan su fruit yadan tsaya suka saye a hanya sanan suka karaso gida Daga Anty har maryam sun matsu suji ya akayi da suka fita, tare zuwa masallaci da,Assalam, Kayan fruit din suka shigo dashi nikiniki a cikin ledoji ,, Maryam wace tafito cikin kwaliyar ta ko kallon su batayi a da suka shigo gidan, Da kanshi ya nufi har gurin fridge ya aje kayan a hankali daidai lokacin Anty Dije ta sallamay tafito, daga daki Yadda taga Maryam tayi mai sai kawai bataji dadin hakan ba, Daki ta shige abinta don makada asata wani aikin, Dakun Anty ta fado rai bace sanan tahau surfanta da sababi, Maryam ta bude baki da zumar yin magana hannu Anty tadaga mata alamar batason jin komai daga gareta, Tace baki da hankali ko wayo zance inba wqutaba yazaki nunawa mutumin da ake fatan shiryuwan shi haka a fili,?? Gaskiya ki gyara hali Maryam don kowa ma haka kike masu, Kada ki kore min jama,a pls, Maryam batace komai ba don tasan cewa yau ta batawa Ànty Dije rai sosai don batai mata fada haka gaskiya, Murya na rawa tace don Allah kiyi hakkuri anty bazan karaba insha Allah,,,,,, ZEEEE MAKAWA,,,,,,👏👏 [2/20, 10:09 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣6⃣ ZAINAIB IDRIS MAKAWA Zaune take a bakin gadon da ke cikin dakin su tai tagumi da hannu guda,shiru tayi sai tunane takeyi Don tunda take da anty bata taba ganin fushinta ba sai yau, Yau din ma akan wani bare kafiri , wanda ba musulmi ba ma, Wai may yasa za,a dinga takurawa rayuwan tane haka akan sai ta yi abinda zuciyar ta bai son aikatawa, Motsin da taji shi ya sanya ta dago kai da sauri don ganin ko waye shigowa, dakin, Anty Dije ce tashigo dakin tana rike da wani dan ledar mai nuna tambarin shago ajikin shi, Yar kujerar dake dakin ta zauna a hankali, tana fuskantar yar kaunar nata wanda tun dara bata fito ba, A hankali Maryam din ta dago kai karo nabiyu takara kallon antyn nata, sai kuma ta sunkuyar da kanta kasa tana kallon kasa, Cikim natsuwa Anty Dije ta fara magana maryam don nai maki fada yau shine kike fushi, Kinfi son in barki ki dinga yin abinda bai dace ba ko yau she, ? Dago kai maryam tayi da niyar yin magana suna hada ido dayar nata,sai kuma ta kasa fadin abin da tai niya, Indan har kinga cewa wullakanta dan adam na da kyau sai kici gaba, Tanafadar haka tamike tana cewa sai kizo ki ci abinci in kinga dama, Dago fuska tayi caba caba da hawaye, ta dubi yar nata tace, Murya kasa kasa tace nifa ba fushi nakeyi ba anty, Fuskan Anty kumshe da murmushi tace Allah ya kyauta amma dai gaskiya ki gyara hali duk wanda zo gidan nan sai yai min korafi akan halin nakasa irin naki maryam, A dan tsorace ko mamaki tadago fuska, takalli yar uwan, Kuka tajeyi a hankali irin na bantausayin nan tace yanzu anty nice mutane kewa korafi, A ranan wuni zungur maryam tayi a daki tana ta faman fushi da kowa don har Issalam mutumiyar ta bataga fuska ba,,, Tunda safe tafito itace farkon fitowa tsakar gida tafara shara da kokarin dora masu abin kari kamar kullum, Saida anty Dije tagama duk abinda takeyi san nan ta fito waje tasamu yar uwar ta tana Sun gaisa kamar wani abu bai faru ba a tsakanin su, A tare suka kara aikin sanan maryam tai wa yara wanka kamar yadda ta saba yi, Tuki yakeyi akan hanyar shi ta zuwa Lagos gaba daya hankalin shi naga tunanen Assalam Yaro karami ya iya yin alwala batare da ankoya mashi ba, A hanya ya tsaya yaiwa kakar shi da Ejoma da suke zaune tare da shi a gidan shi na Lagos, Tsaraba, a wani dan kauye da ake tsayawa kafin ashiga garin, lagos, Tunane ya cigaba da yi na yadda zai, yi da mahaifin shi, Don kwata,kwata baya son zancen kakar su a rayuwan shi, Wanda shidai a iya zaman su yasan cewa mutumiyar kirki ce ita, Ya iso gari lafiya saidai yasamu G/ma bata jin dadin jikin ta, A yadda Ejoma ke fada mai tun wucewar shi kusan sati ke nan G/ma bata jin dadi amma ta hana a fada mai, wai don kada yadamu, Wanka yayi ko abinci bai tsaya yaci ba tashiryo cikin waso kananin kaya sai kamshin turare ke tashi Mama dake zaune saman kujera two siter yazo inda take ya zauna asaman hannu kujerar da take yadan rankafo kanshi saman kafadar ta kadan Yana tambayar ta a hankali ki may ke damun ta sai ce mai tayi batajin komai ita, Cikin dabara Joseph ya lalaba yar tsohuwar suka tafi asibitin da yake zuwa, Likita ya dibata da kyau inda yace ba wani abu damuwace ke da munta kawai sai dai yadan rubuta mata yan magananuwa don tasha, Bayan sun dawo gida dakanshi ya hada mata tea mai kauri ya hada da maganin ta yakaimata, Zaunawa yayi gab da ita yana dan bata a hankali har tadan samu tasha, Alokacin yadan mike tsaye da niyar barin dakin don yaje yadan huta, saboda yana tare da gajiya, Hannun shi mama ta riko da sauri ya jiyo don yasan cewa da magana kenan, Komawa yayi ya zauna gab da ita saida suna fuskantar juna a wanan lokacin, Fuskan yar tsohuwar fam da damuwa tace My child something bad wan happen to you, Joseph yadan kamo hannuta ya hade cikin nashi yana yar murmushi yace, Mama nothing will happen to me just cool your mind pls, Tace it ,will ,my son I see am in my dream, Dariya yakari yi mata yana mai rungumota zuwa jikinta, Kalamai masu kwantar da hankali ya ke mata don yaga cewa ta saje zuciyar ta, A hankali ya mike ya kamata zuwa kan gado ya kwanatar da ita tare da jawo bargo ya rufa mata, A,hankali yabar dakin yana mai rufo mata kofar dakin, Saidai may yana fita daga daki sai kuma maganar mama ya dawo mai sabo a zuciyar shi, Fridge ya nufa yabude yadauko giran ruwa mai sanyi ya dan kwa kwada, Hakalinshi a tashe don yasan cewa akwai abinda ke damun mama din saidai ba zai so ji ba don shi bai yarda da camfi ba rayuwan shi sam,,, Maimakon ya shiga dakin shi kamar yadda yai niya sai kawai yasamu kan shi dazama saman daya daga cikin kujerun dake falon, Yakai wani lokaci a gurin zaune yana tunane shi kadai bakajin karar komai a falin inbada na,urorin daje ta aiki a cikin falon, Azuciyar shi yake tunane don yasan cewa maganar irin su mama ,g tasu al,adan ba karamar magana bace, Da wuya su furta bai faru ba, to amma shi gaskiya har yanzu bai yarda da zance tsafi ko kuma wani believe ba can, Yakai wani lokaci gurin zaune yana iya na,zarin shi akai, Daga karshe dai ya mike jiki ba kwari ya shige don ya kwanta, Abakin gado yake a cikin shigar shi ta kayan barci bayan yagama komai, ga irin al,adan yakeyi kafin ya kwanta, Bible ne rike a hannu shi gwiwowin shi suna kasa kan shi a saman gado idon shi a rufe yafara jero addau,oin da yasaba yi kafin yashiga kwana Saidai wanan karon ya dan sauya addua,n shi bakamar yadda yasaba ba, A hankali ya mike zuwa kwanciya saida a lokacin kuma watan shi tai kara alamar sako ya shigo mai, Samuel ne ke sanar mai cewa Dad na fada dashi cewa anfada mai wai Joseph din yatafi gurin Abdullsamada Mamaki yayi so sai dajin haka don haka sai yai alwashin cewa daga wanan karon ba zai kara, daukar zance Dad ba na hana shi yin alheri ga duk wanda yaga dama nan gaba, Abdulsamad wanda ko ganisa mutum yayi bai san shi ba,a da dole ya tausaya mai, Balle shi da yagirma a gaban shi Shi agare shi may,ye amfani samun mutun ace bai iya taimaka wa na kasa da shi, Gaskiya duk abinda zaiyi wanan karo saidai ayi ta don dai shi yayi niyar tallafawa Abdullmalik din, Da wanan tunanen a zuciyar shi ya kwanta barci sai juyi yakeyi a tafkeken gadon nashi, Aisha wace tai shawaran zuwa Lagos gurin Joseph Don dai tagane cewa idan ta cin mai can tafi samun kudi, bisaga in yazo nan garin Don anan mutane sunayi mai yawa ga bukatun yau da kullun,,, Saidai tayi rashin saa yace mata aranan ya wuto zuwa kaduna don halartan wani taro da zasuyi akan karin farashin da,suke son yi Bata hakkura ba don haka kaduna tasamay shi Saidai yana gurin meeting a lokacin don haka driver ya tura yadauko daga tasha zuwa inda yai masauki,, Sai gab da magriba yadawo yace ta shirya su, wuce zuwa Abuja yanada uzuri kala,kala acan don haka ba zai samu damar tsayawa kaduna din ba,,, Waya yakeyi alokacin don haka sai yaga kawai Aisha tana kokarin har hada kayan ta, Yana gama wayan yakai kallon shi gareta yace, sai naga kamar lokacin sallah yayi ko,? Bazakiyi sallah ba kafin mutafi, inafa zai fi maki don sai dare nasan zamu karasa, Tana wani jan kafa kamar bata son yin sallah a lokacin, Har ta idar yana zaune sai dan,ne danen wayar shu kawai yakeyi, Duk da bawai yasan ya ake sallah ba yadai fahinci cewa batai wani dadewa ba a gurin yin sallah, Don haka da mamaki yake ce mata har kin gama ko,?? Don haka mikewa yayi yadauki duk wani belongings na shi dake daki zuwa waje, Sai cikin dare suka samu isah don haka masaukin shi ya wuce direct, don KB yasan da zuwan shi, Yasa an gyara komai duk da dai dama gidan kullun acikin gyara yake, Shikan Joseph suna isa a cikin daren nan fita yayi zuwa gurin wani mutum da yake son gani, Aisha tun tana jiran shi tana yar tsuki, har barci ya dauke ta, bada sanin ta ba, Kodo Joseph yadawo yasamu tayi barci don haja ko take away din da ya zo masu dashi batasamu ci ba, Kiran sallah da akeyi daga wani unguwa wanda da alama ba nisa daga gidan Joseph din shi yata da Joseph din a lokacin wanda dama al,adanshine haka duk wani Christian mai rikon addini yana tashi daidai wanan lokacin, Don yin morning prayers din su kullun, Aisha tana kwace shemay shamay saman gado, tana barcinta abinta, Yar rigar barcin da tasa don daukar hankalin Joseph, har barci ya kwashe ta yadan kware gefen ciyar ta a fili, Don haka yana fitowa yin burshe, ya isa har bakin gadon inda ake kwance ko motsawa batayi ba, Yana mamakin wanan irin barci haka ace mutum bai tashi ya yi morning prayer, haka, Hannu yakara kaimata yana dan dukar cinyar ta data dan kware wurin barci, Yana cewa baki tashi kiyi salkah kadafa time ya wuce ki, Sai wani mika takeyi shiko sai kallon mamaki yake mata alokacin Yaga cewa ai Assalam yarone amma duk yake tare dasu akai kiran sallah Zakaga yaron na kokarin tashi zuwa yin sallah, Amma ita gata da girma ta yaga bata damu da ta tashi yi ba,,, Kallon inda yake tayi ido tafa da kwana, tace mai kabari kawai inda na tashi ai zanyi, Wani irin mamaki ya kama shi azuciyar shi yana mai cewa O God help me with dis , Aisha sallah ma bazaki tashi kiyi ba sai kinga dama, Haba kiwa kanki fada mana ai dis is bad wlh, abindan lokaci kadan,, Tai wani mika badon taso ba ta tashi buguzun,bugunzun zuwa cikin bathroom, ko minti nawa bata kai ba saigata tafito wani dan yalalon gyale ta yafa Joseph wanda yai daidai da gama addu,an shi ya na kokarin rufe Bible din shi ya kalle ta yana mai kada kai cikin mamaki don ganin gyaken da ta yafa wai zatai sallah, dashi, Kwanciya ya yi rigingine ya kallon yadda take dangwara goshi kamar wace keda wani uzuri ,a gaban ta, Ba,afi mintuna ba ta sallamay tafado mai saman gado gaba dayan ta, Kokari takeyi ta fara romancing din shi sai yai dabara yadan jaye ta daga jikin shi yana nai ce mata zan dan fita jugging ne yanzu kafin gari ya haska, Yajaye daga jikin shi yana mai kojarin daga wa don ya sauka saman gadon, Sunan shi takira cikin wani irin muryan yaudara idon ta ya canza kalla a lokacin, tana mai ce mai Wai may yasa kake min haka ne pls ta ya zan bata time dina zuwa gare ja amma kai kullun sai ka kawo min uzurin da baikai yakawo ba, Tana kokarin kara jawo shi zuwa gareta yai saurin karasa mikewa daga saman gadon Yana maice mata ki tambaya kiji ni Joseph ba irin wa yan nan mazan bane da kike tsan mani, Wanan ma da kikaga ina maki just don kada kiga kamar banda,time dinki ne, Amma tunda kinga hakan ma bai isheki ba Ya nakai kofa yace pls ki daina zuwa don hakan ma na itmya jamin matsala, Mamaki da tsoro kalaman shi suka jefata ita Aisha,da mutum nawa ke kokarin kawa gareta ne yau har wani ke fada mata haka, Inbadon tasan cewa tana moriya dashi ba ko a haka da yagane cewa tawuce wanan kalamin gareta,,,, Bayanshi tabi da kalllo har yabar dakin cikin shirin zuwa dan motsa jiki, Hmmm Aisha bata san waye Joseph ba da batai tunanen hakaba daga gare shi,,,,,,, ZEEE MAKAWA [2/20, 10:18 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Alhamdullah jerabawan su maryam yafito yanzu ,yaya I,lliyasu ya samo mata guri bi karatu,a FCE kwantagora, inda zata karanta bio,chemistry, Maryam taji dadin wanan abin so sai ba maryam ba kawai har baba Don har gida yazo yai ma Anty Dije da mijin ta godiya akan kula mai da yar shi da,sukeyi tsakani da Allah, Maryam wandda yanzu girma da wayo yazo mata ta roki Anty ta barta taje gurin mamanta, acan Bobi kafin ta fara karatu, Anty bata kiya ba saida tace sai ta fadawa baba don kada, yazo yaji daga baya yai fada Baba bai,yi fada sai fatan adawo lafiya da yai mata yabata dubu daya yace tasai masu tsaraban man shafi da sabulun, wanka, Cikin kwana biyu akai mata yan shirye,shiryen tafiya, Duk da bawai maryan ta saba da mamanta bane amma dai tai ta zumudin zuwa kauyen,don tagane su,,, Ranan da zata tafi tunda safe ta hana idon ta barci don zumudi, Har saida Anty ta kasa kan,newa tai mata, magana Maryam wai,dama dai ashe kin dade kina son yin wanan tafin ne ko, Yar kunya taji da kuma nauyin Anty nata, saita dan sune kanta tace ,aa anty kawai dai ina son zuwa ne inga yadda garin yake wallahi, Har inda zata shiga mota Anty ta rakata tare da yaran su,, Inda yaran ke kuka sai sun bi little mummy su inda zata, Shiru take zaune cikin mota sai tunane takeyi yadda zata riski mahaifiyar ta , Don dai tasan cewa zaman kauye na maida mutum iri, sai tausayin mahaifiyar ta ya,kamata Tace Allah sarki mama ita kuma nan Allah yai nufin zaman rayuwan ta, Haka tai ta tunane azuciyar ta har suka isa garin kamfanin,Bobi, saidai tai mamakin ganin garin a saman babban titin zuwa minna da kwantagora, Tana sauka idon wa yanda ke zaune a bakin titi yayo kanta caaaaa Wani yaro tagani ya tafiya sai,tai mai sallama nan take tambayar shi gidan liman hamza,nan yaron yai mata kwatace akan tabi wani dan lungu, zata ga wani gida mai katon icce a kofar gidan tashiga nan ne gidan, tana bi kuwa sai gata a kofar gidan,, Da sallamar ta tashiga mata uku tafara gani su guda tana daka guda kuma tana duke tana wanki dayar kuma tana wanke wanken kwanoni, Duk kan su daurin zani agaba, ga yara manya da kanani nan jagwal da su, wasu majina ahanci wasu kuma kunu ya bushe masu a baki har hanci,,, Sun karba mata sallama cikin mamare ki wace don ganin tada sukayi da kaya a tare da ita, A cikin ladabi ta durkusa har kasa tana gaishe su , Abin mamaki sai ganin mata takeyi suna bulowa daga wani dan lungu, ashe ganin tsoro taiwa gidan matane, ciki fam kusan su goma, A cikin sanyi muryan nan nata take cewa, don Allah mama Rukaiyan saleh nake nema, Wata mata wace ke daure da wani zani blue mai photo barewa ce tace taufa gani nan, Sai wata wace ke gefe tsaye tun shigowar shin kodai Mamuce,, Maryam tace maryam ce sai salati suka hau alokaci guda, Suna murna da farin cikin ganin ta, cikin sauri suka fara kwasan kayan ta zuwa ciki dashi, Maman ta tace a kai ta, dakin abokiyar zaman ta, wace suke cewa Ladi, Anan akai mata masauki ita, da kayanta, kafin wani lokaci har an kewaye ta da abinci kala kala, Da yake kauye ne duk sunyi abin sanar su tasayarwa, Kwarai mahaifiyar Maryam taji dadin ganin Maryam, da kuma wanan ziyarar da takawo masu, Bayan kowa ya watse akabar Maryam da mahaifiyar ta, a hankali maryam ta dago kan ta takalli mahaifiyar ta wace ke tsugunne a gefen dan gadon ta,, Tace mun samay ku lafiya mama, cikin kariyar murya take maganar kamar wacce zatai kuka alokacin, Mahaifiyar tace takauda kukan da cewa yasu wajen yayan naki ina fatan duk kuna lafiya ? Kikara rike yar uwar ki da amana kin daiga yadda itama tarike ki amana, Ba maicewa ga yadda kuke da ita ,don ko da nake nan ina jin irin zaman da kukeyi da ita Duk wani abinda ta hore ki dashi kiyi kokarin rike shi, Allah ne kawai zai iya saka mata da alherin sa,, Saidan hiran sauran jamar su da sukayi inda take tambayar ta ko kwana nawa zatai masu ta sheda mata sati guda zatayi ta koma, Daga karshe ta gabatar mata da tsaraban da tazo masu dashi Nan mama tai filla,filka da kayan saida ta,tabatar dakowa na gidan yasamu tsaraban, Maryam taji dadin zama tare da mahaifiyar ta duk da a kauye suke sam bata nuna masu kyama ko nuna wayewa, Dan zamanta har da karatun addini suka dan samu daga gareta, Duk safe za,a kawo mata abin kari daga ko wani shiya nagidan hakama da rana ko dare kowa da kwanon shi da zai aiko mata, Ana gobe zata koma har daga makwabta aka dinga kawo mata tsaraba irin na kauye, Badon sun so ba washegari tabar su takamo hanya dawowa ita kadai, Tunda motar ta tashi sai taji zuciyar ta duk ba dadi ya cushe mata guri guda ji take kamar kada su rabu da su,, Hannu tas tadan share hawayen ta da taji yadan gangaro mata, Sannu a hankali sai gasu Allah ya kawo su cikin gari lafiya, Zaune yake a kofar gidan su Anty dije Assalam na rike a hannu shi yana yar wasan lilo da hannu Joseph din, Mai mashin din da ta hau ne yazo har kusa da inda suke zaune, Ido yabita dashi har lokacin da ta sauka ta mikawa mai mashin kudi, A,lokacin mai mashin din ya sauke mata wani buhu,da ke shake da kayan tsaraba da tazo dashi,,, Joseph ya sauke hannun Assalam a hankali shiko Assalam naganin ta yaje ya kankamay ta ya,na, ihun da murnan ganin ta, Suna can suna murna basu san lokacin da Joseph ya dauki buhun kayan da kuma yar trolley din ta zuwa cikin gida, Saida suka gama ihun su koda zasu diba basuga kayanta ba ,kuma basuga Joseph ba Sai ganin shi sukayi ya na fitowa da ga cikin gida, yana kakabe hannun shi, da handcarchef, din shi,, Da mamaki take kallon shi don sam,batai tsanmanin cewa zai iya daukar mata kaya dakamshi zuwa cikin gida Juyawa tayi daidai lokacin da ya iso inda suke tsaye, cikin yar karamar murya tace ta gode duk da tasan cewa bawai dole bane ya amsa masu, Tadawo da sati tafara shiga makaranta daukan lectures, Maryam yarinyace mai hazaka ga karatu dama duk kowani famni ba,abarta a baya ba, tana kokartawa, San,nu,a hankali kanta yafara wayewa kamar kowace budurwa da ke makarantar, Yau ma kamar kullun shiri takeyi don gudun makara,,saboda tasan cewa suna da lecture din wani bakon malami da zai dauke su, Gashi sun samu labarin cewa baida wasa ga aikin shi duk wanda yazo bayan shi bazai shiga ma aji ba alokacin kuma, dole kowa yasai handout din shi, Yau har da break fast anty tayi da ita ta tsaya tasha amma maryam sauri take yi tace idan taje can zata samu dan abinda taci, Ta dade a bakin titi kafin ta samu abin hawan da zai kaita amma sai suce bazasu je har can ba yanzu da safen nan, sai da kyat tasamu wani yace zai kaita a dari biyu tace ba komai,su tafi,, Hakan ya jawo mata makar har time din da za,a fara lecture din yadan gwauta da minti biyu kacal, Amma jin cewa da tayi ance baida sauki lecturer din wurin rashin nasiha, Yasa taja baya kawai tasamu wani mota ta dan kwanta saman motar, kadan Rayuwar ta yai matukar baci sosai da rashin samun wanan lecture din da batayi, Tana tir da halin rashin imani,ko, nasiha nawa su, mutane, Tsaye yake kanta yana magana amma Maryam batasan cewa, da mutum yana mata magana ba, alokacin, Motsin da taji ne kamar kusa da ita shi yasanya ta dago kai da sauri don gani kowaye gurin, Wani black, handsome guy ne tsaye agaban ta,sajen fuskan shi yah karawa fuskan shi wani daraje,da girmamawa, Cikin shigar dinkin shadda yake,dinkin wanda ya tsaya mai,daidai ciyar shi sai guntun hannu, da a,kaiwa dinkin, Yana saye da wani farin glass wanda bazata iya tamtace, ko na magani ne ko fashion ne kawai, Duk da indon shi nada glass bai hanata,gani kwayar idon shi ba da kuma kallon mamakin da yake mata, Batasan lokacin da taisauri ta mike ba daga kwanciyar da tai, a saman motar mutane, Yana tsaye hannayen shi rungumay a kirjin rungumay Ganin ta tashi yasa yai saurin kokarin wuce wa, Saida kuma yaji ta saki wani dogon tsaki, tare da yin kwafa, Dawowa yayi yana ce mata lafiya dai ko naganki a haka, ko kina son wani taimako ne, Dan tsaki taja tana kokari gyara jarkar dake rataye a kafadar ta, Wani mugun malami ne yabata min rai don yaga Allah yabashi baiwa ya,manta cewa wani dama ne ubangiji yabashi Saiga shi ,shi yana amfani da damar yana cutawa diyan mutane, da, damar ta shi Tadan daga kai a karo na faron tunda tafara mai magana cikin bacin rai, tace ,, Wai ace duk samakon danayi don kada in makara, shiga,lecture din shi, saboda ance shi mugune in,,, in an, makara bai bari mutun yashiga, Sai ga shi,,abin hawa yabani matsala wallahi, Amma abin haushi wai minti biyu kacal na dora a saman lokacin da ya,fara lecture, Sai,gashi wai ya rufe ba mai shiga kuma,,Abin haushi ance bai yiwa Allah don mugganci, shi, Tun da tafara fuskan shi na a,kanta, Fuskanshi dauke da murmushi yace too bad, Is alright, may sunan guy din ne wai,,, Ido ta,dan zaro waje tace kai may ye, zakai mai wa yanda ma suka dade tare dashi sun yaba shi da mugun hali ,,, Fadamin sunan shi kawai ko zan iya taimaka maki akai, Taidan wani far da ido taba alamar tunane, can tace, Hmmm wai,ko A,A, MASUGA suke ce mashi ba, ko wa ma something like dat dai, Ya na kokarin bude motar shi, yakalle ta ido cikin ido, yace mata,, Ok ki,samay ni a block C idan kin,je office na uku daga daman ki, ,ki shi ga zaki samay ni, ciki,zan yi kokari in gani, may za,ayi akai, Bawani jin darrr ko kuma tunane, wani abu dakaje yadawo, gareta, sai cewa tayi, to kawai ta amsa mashi alokacin, har yashiga motarshi yana kokarin tayar wa, Sai bayan ya wuce ne tai dan ajiyan zuciya cikin bacin rai tace shikuma wanan din ma kowa ye a makarantar da zaice, zai tunkari, AA Masuga, Tunda duk sakkon datayi tun da farar safiya ya hana yashiga ciki, Next lecture tashige abinta batare da ta damu da zuwa gurin da ake jiranta ba,,, Don ita a ganin ta mugun malamin ya riga ya cuce ta ko,, Zaune yake yana aikin tura sako a cikin system din shi yanayi yana gyaran dan farin glass din da ke man,ne a fuskan shi, Saidai a cikin zuciyar shi maganganun yariyar dazu ke mai yawo a kwakwalwan shi, yana jin muryanta tana fadin ,,,, Allah yabashi dama saidai shi yana amfani da wanan baiwar yana cutar, da,diyan mutane dashi, Yau ko karyawa ban tsaya nayi ba saboda kawai in,samu shiga kafin time din shi yayi sai,dai abin hawa yaban matsala saboda, minti biyu, kawai kacal, na kara Shine ka gan,ni ana ya hanani shiga, saboda daukar alhaki A cewar wanan yarinyar da ke ta fadamai magana tsakani da Allah Kai ya girgiza da yakai nan yana mai furzar da wani irin iska daga bakin shi, A gaskiya wanan maganan ta soki zuciyar shi don dan abu kadan kejawa mutun matsalal rayuwa, Shi baiyiwa mutane uzurin matsalal suba taya shi Allah zai sa wani yai mai nashi watarana, Idan ma har bai yi nasiha ba sai wani yazo yayi don komai dadewan ka a wuri dole watara bakai, bane a gurin,,, Ire,iren wanan tunanen yadinga yi a zuciyar shi yanayi yana kallon agogon dake daure a dogon hannun shi, Dan tsaki yaja don rashin ganin yarinyar batazo ba balle ya karasa jin korafin jama,a akan shi,,, Maryam ko wace sai kusan uku na rana tasamu kan ta sai a lokacin ta tuna cewa ,wani yabata appointment dazu da safe, Bashiri cikin sauri tajuya zuwa block din da aikai mata kwatance, A hankali ta kwankwasa kofar office din yana zaune hankalishi naga aikin da yake idon kafe da farin glass din dake idon shi, Batare da yadago kai ba yake cewa mai kwan kwasawar come, in, batare da yadaga kai ba still Da sallama abakinta ta shigo office din wani irin sanyi da kuma kamshi, turaren maza na Minkaeel, ne , ya,daki hancin Sai da yaji muryan mace ce yadan dago kai yaga kowace,ce har zai maida kanshi ga abinda yakeyi Ido biyu sukayi da maryam wace ke cikin shigar doguwar jallabiya sai dankwalin da ta yane fuskanta da shi, Wanda iya round din fuskantà kawai zaka iya gani ,duk sauran jikin ta a rufe yake lif, A hankali cikin dishasshiyar murya take gaishe shi cikin ladabi, System din dake gaban shi yadan rufe kadan ya na mai fuskantar ta, Cikin kujeru biyu dake office din suna fuskantar wanda yake zaune ya nuna mata, Malam kayi hakkuri pls sai yanzu muka , fito, daga lectures, Cak taji numfashin ta ya tsaya daidai lokacin da tai tozali da wani dan prem dake kafe a gaban tebur din shi An rubuta da wani ruwan gold cikin wani sallo A,A MASUGA,,,, ZEEE MAKAWA,,,, [2/20, 10:24 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, A,A masuga ido ya kura mata batare da ya dauke kan shi ba don ganin irin re,action din da tayi lokacin da idon ta yakai ga prem din, Murmushi yayi yadan gyara zaman glass din dake idon shi, dai dai lokacin yake ce mata, A nutse, ya,ce,ya, sunan ki malama,, cikin wata irin tsadadar murya yake magana kamar bai son yi, Kusan minti uku bata iya cewa komai ba har lokacin Murmushi yayi shi ya fargar da ita daga dogon tunanen da tafarayi naganin gata a gaban hukumar makarantar an gurfanar davita akan sai takawo shedan cewa A,A masuga mugune, Kara tambayar ta yqi yana mai cewa ,cewa nayi ya sunan ki ne, ? Murya kasa,kasa ta furta cewa Maryam Abdullahi, Bobbi, Jin yayi shiru tadan dago kai ta kalli inda yake cikin sauri ta dukar da kanta, Don shima din ita yake kallo a lokacin, A,dan kunyace ta furta don Allah kayi hakkuri ban san,,,,, Hanni yadaga mata yana mai gyaran murya yace Naji duk bayanin da kikai min dazu akan AA masuga Maryam wace kan ta ke duke sai a lokacin tadan dago kai takara kallon shi a karo na biyu don jin da tayi tace A,A masuga, Azuci kuma cewa tayi jidan rainin wayo ko har yanzu yadauka ban gane shine ba yaci gaba da shanmata na ,, Kamar daga sama taji ya kira sunan ta in full, Adan tsorace, ta dago kanta, saidai wanan karon fuskan shi a daure take tamau, bakamar dazun ba, daya dan sake ta, Kai ta mayar kasa don ji takeyi gaban ta yana ba da dammmm, Yace, naji dadin wanan maganar da kika fada min da don tun da nake ba wanda ya taba fada min cewa abin baidace,ba, Nikuma azato na hakan taimaka wane ga dalibai, ban yi la,akarin cewa zai iya illikanta rayuwan wasu ba, Kokuma in ci hakkin wani ta irin hakan da nakeyi , Yace kin san may ? Kai ta dake kasa, ta girgiza mai,, A hankali yaci gaba da mata yan tambayoyi , saidai wanan karon a kunyace take bashi ansa, Sallama tai mai gami da bashi hakuri, Yace haba dai ita taimakon shi, ta tayi tunda har ta iya fada mai gaskiya,,,, Shiru yadan biyo baya sai shi A,A din ne ya ita cewa muje in kaiki gida don time yayi ko , Don kada ki rasa abin hawa, A ranta tace wake kai ta gida da, da bata dare, Amma a fili dan murmushi tayi, tana mai cewa da kabar shi ai zan samu bus, Batare da yai magana ba ya mike tsaye, yana mai hada yan tarkacen shi a cikin yar briefcase din shi, Maryam tarigashi fitowa yana biye da ita a baya don sai da ya tsaya yadan rufe office din shi, Amma may suna fita fafir Maryam tace yabar shi kawai bazata shiga ba, Saida ya nuna mata cewa bai son jayayya, sanan ta daure suka tafi, a cikin motar shi, kirar Peugeot NEW MODEL,,, Tafe suke ba mai magana acikin su sai dai kidar da ke tashi a motar na siliado, Sun kusa shiga gari ne yadan joyo inda take yana cewa, Wani unguwa zamu tafi ne, ? A hankali Maryam tace furta da ka sauke ni a round about kawai sai in karasa, Batare da bata amsa ba ko tsaya yace wani unguwa pls, ? Cikin ,ciki ta furta kwanar kuka, Kwanar da zai sada shi da unguwar ya karya, daidai kusan uguwar ya ce gidan wa, Illiyasu costume, kallon ta yakarayi da kyau don jin gidan da take, Yace ke kaunar matar shine ko, kai ta gyada mai a hankali, Daidai kofar gidan ya aje ta, Ya ce toh nagode, maryam da taimakon da kikai min,yau, In sha Allah zan gyara ga dalibai zaku samay ni masauki da rangwamay, Kan ta na kasa cike da jin nauyi, A hankali tace nima nagode malam da fahintar gaskiya da kayi, Murya cike sa cike da amon murna yace ai ni ban san may zan kara fada kuma, Ta bude gambun motae a hankali tafita shi kuma a hankali ya fara ribas da motar shi, A nutse ta rika takawa har zuwa kofar gidan su, inda taga wasu a zaune, saida sun bada baya, Kallonta yayi a glass din motar har tashige shi kuma ya harba yabar shi yan, Zuciyar shi fam da tunanen kalaman yarinyar, Har ta shige gida batare da ta lura da wanda ke wajen gidan nasu ba alokacin, Shigewar ta yabi bayanta da kallon mamaki a ran shi yana mamakin yau she tagirma haka, Maryam na shiga gida tasamu Anty Dije, tana aiki, taimata sannu da gida tafada Wanka don ta dan ji dadin jikin ta, A marairaice maryam ta ke cewa Anty Dije, kamar mai shirin yin kuka Anty tunda safe banci komai ba tun da na fita gida, Yar karamar harara Anty ta sakar mata tana cewa, ,oho maki, danace ki tsaya ki karya ba ki ,kikayi ba waike kina dokin zuwa makaranta, Yar guntuwa tsuki tayi tace kuma wallahi duk sakkon danayi ban samu lecture din ba anty, Baki Anty ta tabe mata tace anfada maki ana samu cikin zafi ne, Aikomay zakayi kayishi a cikin hankali, don rashin cin abinci na iya jawo maki ciwon ulcer, Falo tadosa don ta zauna ciki ta ci abincin ta tana kallo, Ganin mutum tayi a zaune yana cin abinci shi a hankali, Juyawa tayi da sauri da niyar barin falon a lokacin, sai kuma tatuna cewa ba su gaisa ba don haka ta tsaya cikin ladabi tace mai ina wuni, Da wata irin dasashiyar murya ya amsa mata, a hankali, Sai ta juya kawai tabar falon ,shiko mamaki yaji kwarai da gaisuwar da yasamu cikin mutunci gare ta yau,,, Wanan shigowan da su Joseph sukayi tare da abokan ahi shigowa ce ta musam man sukayi Don bukin sallah da za,ayi inda matasa ke bukatar a bukin hawan dawakai wato Dubba, Don haka basu samu wani zama ba sosai kamar yadda suka saba, Don yawan zirga,zirgan da suke yi tsakanin birni da kauye gurin ganin cewa komai ya kammala, Yau ma kamar kullun sun dauke shi zuwa wani kauye duk da shi kauwaici yake masu don ganin cewa suna kokarin sashi cikin al,umurorin su, Amma shi gaskiya duk irin wanan abin bawai yadamay shi bane shi harkokin business din shi kawai ke gaban shi, Amma a zuwa yanzu abin da yake gani gurin su jibrin da KB dama sauran abokan su yana bashi sha,awa sosai , Duk masifan da mahaifin shi zaiyi yayi mai sunyi mai preaching kala kala akan ya daina bin diyan musulumai, Kawo yanzu, Yasa an gyara mai gidan mahaifin shi amayar mai dashi hawa biyu sai kuma katon parking space mai girma da saura guraren da ake samu masu kawata gida, Amma duk wanan baisa Mr Ema kyale dan nashi ba, da fitinar ya daina tallafawa mutane musanman musullumai, Yasa ma Joseph din ido ne kawai don yasan cewa Joseph din yanzu ya wuce sanin shi, Wanan hurda da kuma al,adun da Joseph keyi na hausa baima ma Mr Ema dadi sam, Yau ma kamar kullun cikin fushi yake wa dan nashi fadan cewa yaran hausawa sun asirce shi ne, Saboda labarin dayazo mai cewa da gudun mawan Joseph acikin wanan gagarumin bukin da matasa ke ta kokarin hadawa don cigaban masarautar su,, A fuce yace baya son Joseph ya kara zuwa garin yafi bukatar ya daina zuwa da ace yazo yana hurda dasu haka, Wanan maganar harta kai Joseph yai yun kurin gina gidan shi inda zai dinga sauka inda yazo, Sai da baban yaga cewa zaiyi hara sosai ya kuma kara bidan dan nashi sulhu, Inda ya ke sheda mai cewa hausawa shu,uman mutane ne yana gudun nan gaba ne kada su ja,ra,ayin shi akan wani abu can, Maryam wace yanzu, haduwar ta, da A,A MASUGA, yazama mata, wani sanadin alheri, Don kwana biyun nan shi ke, zuwa da kanshi ya diba yagani ko ya karatun ta ke tafiya, Tun maryam na dari,dari har ta fara dan sake jikin ta dashi suka dan fara sabawa, Duk wanda yasan Maryam ada yanzu in ya ganta bazai sheda cewa ita bace saboda, Tazama cikakiyar yar jami,a saidai har yanzu wanan hali nata yana, nan kamar da ba ta yawan kula samari kamar sauran yan mata, Mutana suna zaton cewa ita, sister din A,A masuga ne, Saboda yawan ganin da ake masu tare ko kuma yawan kulata da yake yi,, Kwanan nan gidan Anty Dije cika yake yi sosai sasboda gab suke da fara program din su Duk may neman Joseph indai yana cikin garin kwantagora a gidan anty dije zai samay shi saboda bai son su samay shi a gidan baban shi don gudun fitina, Tafe suke tare da A,A masuga,,,,da wani abokin shi,, acikin motar shi sai faman waya yake, yi da alamar da mutanen gidan su yake waya don yadda taji yana bada ansa yasa tagane hakan Yana gama wayan yai yar ajiyar zuciya tare da shafo sumar kan shi tundaga, fuska, zuwa baya,har kusan wuyan shi,, Sai a lokacin yadan waiga inda maryam ke zaune hankalinta a titi, tana kallon yadda abin hawa suke ta zirga zirga kasan cewar yamma tayi a lokacin, Maryam ya furta a kasalance kamar yadda yake kiranta kullun,, Wanan, kiran shi ya,katse mata kallon titin da take yi tun dazu, May yafaru naji kin yi shiru, ko , yadan kalle ta na minti guda, Cikin nuna kulawar sa yace kan ki na ciwo ne, naga kin yi shiru, Kanta ta girgiza tace a,a babu wani ciwon kai , Illa masu son yin bukin nan dake son takurawa rayuwan mu, Ace bamu da hutu sam a gidan mu in har wanan dan Christian din yana gari, Baki makam A,A masuga ya tabe yace lalai kam ku samu aiki, Yace wai may ye alakar shi da ku ne, ma wai da naga ya na zuwa gidan ku duk lokacin da yake gari, gashi shiba musulmi ba ba bahaushe ba, Batare da tai magana ba tai dan guntun murmushi irin na iya fuska, kawai, Aiko kamar kar su karasa kofan sai ganin jama,a fam sukayi ana t hayaniya kamar ana wani buki, Da kyat malam masuga yadan samu ind ya Parker motar shi a gefe don tafita, Aiko idon jama,an dake gurin ca,aaa akan motar don suga ko waye zai fito cikin motae, A hankali ta bude marfin motar tare da yin yar guntuwar tsuki wanda duk inda kake zaka ji,ta,,,, Dan harara malam ya watso mata daga inda yake yana cewa In bake ba wake gudun taron mutane ? Batare da tace mai komai ba ta,kauda kai zuwa inda taga su Joseph zaune suna diban wasu takardu a hannayen su, Diba guda tai masu takauda kai gefe guda cike da jin haushi, don wani iri taji a ranta,ganin yadda yake kokarin shige masu, Koda A,A masuga ya tsaida mota tafita , ko kallon inda suke bayi ba nan tabi ta gaban su ta wuce kawai abinta batare da ta tsaya gaidasu ba, Kamar may rada taji ya furta sunan ta a karo na farko ke nan tun sanin tada shi, Wasu takardu yamika mata na cewa don Allah taba Anty Dije ta aje mai akwai wanda zaizo ya karba a gurin ta, Kamar ta wuce don ita aganin ta yama raina mata wayo , A matsayin shi na kafiri, Arne, zaice zai ai,keta sai kuma fadan Anty ya fado mata a rai Dole ta tsaya ta mika hannu ya miko mata, cikin rashin ko inkula, Tana shiga rai a bace ta yi kokarin mikawa anty takardan tai shigewar ciki, Ana cikin wanan hada,hadar shirin hawan dabar da suke yi wanda mutane sun hana Joseph din tare da mabiyan shi shakat, Har su maryam dake tare dashi a gida koyau she zakaji ance ana wai sallama da Joseph din, Ita dai maryam mamaki taje ji na wanan halin da ga mutane na kokari zubar da mutuncin su da Allah yai masu akan kwadai, Don haka ko tana gida bata yawan zama a waje don gudun damuwar jama,,a Yau malam A,A bai zo school ba yai tafiya zuwa wurin wani seminar da zasu a kwara state, Mashi ta tare don komawa gida duk A,A din yace ya hada ta da wani friend nashi ya dinga taimaka mata, zuwa gida, Amma ita maryam din sai taga cewa bazata iya bin wanan mutumin ba don kawai kariyar mutuncin ta, Mai,mashin tatara ta hau, duk da tace mai kada,yai gudu da ita, amma kamar zuga shi tayi a lokacin Haka yakw kokarin wuce motoci da ita a baya makale, Daidai kwanar sabuwar junction suka hadu da motar yan matasan masu tashe agari, Cikin wata jar mota haka kallo guda mai jan motar yai mata,ta kauda kai duk ita ma dai taji kunyar yadda take dane bayan mashi, mai mashi nata,gudu da ita, Kallo mai kamar harara ya watso mata, wanda ita ma din kusan irin kallon ta watsa mai a lokacin, ta mayar mai da martani, Kai Joseph ta girgiza don in a kwai abin da yai hating she yaga mace a saman mashin ana gudu da ita kamar bata san zafin ta ba, Bai san har lokacin da yafurta a fili ba yace nonsense,kawai, A rashi yake tunanen ya furta sai gashi ashe afili ya fadi hakan, Jibrin dake gefen shi ya kyalkyale da dariya yace kaganeta ashe, Kai kawai ya gyada mai alamar eh, a hankali ya furta may ye amfanin hawar mashi a diya mace pls, Maryam ko rana isa gida ta samu anty tasayo zogala, ai cikin murna ta shiga sallah kawai ta idar tafito waje don ta gyara masu zogalar, Bayan ta yanka su albasa, da attarudu da tatasai sai man kulikuli da ta lema masu asaman takawo garin kulikulin ta cakude wuri guda sai ruwa mai sanyi da ta dauko, Da shikafa tai niyar zubawa taci bayan ta debi daidai zamar ta asaman wani tabarma da ta shimfida don ta ci gwaben ganyen, da tayi, Shigowar su ,suma ke nan a gidan, inda, jibrin ke gaba, wani lawal na binsa, sai Joseph tare da wani tajudeen a baya, Shigowar ya fara rage mata dokin da takeyi nashirin cin ganyen da tayi, Jibrin ne da shigowar su , yadan kalli inda maryam take zaune yace mata, Ke ashe har dadi kuke ji indan kun hau irin wanan mashin din dake kusan tashi sama da ku,,, Baki kawai maryam ta hangame cikin mamaki da maganar jibrin, Saidai taso ta furta cewa wani abu amma sai ta kasa, cewa komai don wani irin al,ajibi jin maganar da tayi, Don dai ita tasan cewa ba gwanar hawa mashin bace ko banza Yau ne kawai da take kokarin ganin cewa ta iso gida da,wuri don ranan da yai yawa a garin, Ji tayi wasu hawaye masu dumi sun gangaro mata a fuskan ta, ga wani malolon bakin ciki da ya tokare mata makogoronta, Takai wani dan lokaci a gurin zaune takasa tashi, Saidai tana kiyasta irin daukar da sukai mata a matsayin yar iska kenan ko, Bataji zuwan Joseph da Assalam inda take zaune tana hawaye ba,, sai ganin shi tayi gaban ta, A hankali ya sauka bisa gwiwowinsa, yace little mummy kiyi hakuri amma gaskiya jibrin ya fada maki, Banza tayi da shi sai kuma wani wawan harara da ta sakar mai, har Assalam saida ya dan ji tsoro ya dan shige jikin Joseph,, A raunane ya kara cewa kiyi hakkuri wanan ba abin bata rai bane, Kala batace mai ba sai mikewa da tayi tsam ta nufi kofar da sauri,,,, Ido yabita, da shi don dai shi baiga abin bata rai aciki ba,,,,,,,,, ZEEEE MAKAWA, [2/20, 10:26 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Buki sosai akayi a wanan bukin hawan Dabar da akayi don matasa masu ji da lokacin su sun halarci wanan bukin nadaukaka masarautar kasa kwantagora Wanda ke tatare,da tsohon tarihi acikin ta kamar sauran manyar masauratar da ke a kasa shen hausa, Anbuga a jaridu da kuma sauran kafafen yada labarai, na kasa,, Inda bukin yasamu karbuwa fiye da zaton may karatu, Ana gama wanan bukin da kwana biyu Joseph yabar garin kwantagora , saboda gudun fushin mahaifin shi da yasan cewa yana hake dashi, Duk irin abubuwan da ya wakana agurin duk Mr Emanuel nada labarin komai tankar a gaban shi akayi, duk shagallalikukan Don haka joseph ko kasan bai tsaya ba ketarawa yayi zuwa kasashen waje da niyar yatafi, yadan huta a can, Tun bayan wanan abubuwar, maryam babu ruwanta da zancen, wani wasan da akayi Wanda ita take gani kamar duk wanan abin bai cikin irin tsarin rayuwar ta,, Ita bata masan cewa masu takura masu a gida, basu garin ba tun bayan bukin da gari yayi kamar zai tsage, don cinkoson jama,a Don ganin da su tun zancen da suka ce ta hau mashi a na gudu da ita kamar wace bata san zafin kanta , Ita ko a nata zaton gani takeyi kamar suna ganin cewa bata san darajan kanta ba ne tunda har take hawan mashin da na miji, Idan har ta tuna da wanan kalamin sai taji duk yanayin ta ya sauya,, Saboda ba karamin ci mata fuska take ganun sun yi ba, Takan yi tsuki tace wai gwano baya jin warin sa, su da suke hurda da yan iskan yan mata Shine har zasu samata kazafi akan hawa mashi, idan bata hau mashin ba da may zatai tafiya to,,, Wata rana da la,asar bayan Maryam ta dawo daga wani gida da anty ta aiketa karbo, mata sakon wasu kaya da aka turo mata ta daga kano,gurin wata mata,, Don yanzu Anty tana dan taba business irin da matan gida ke dan yi, Domin kariyar mutuncin su saboda hana, bani bani gurin maigida, Wani mutum tagani dattijo zaune a kofar gidan su, tun daga nesa take kallon mutumin a cikin mamaki, saboda ganin shi da tayi gab da kofar gidan su,, Saboda a gaskiya bata taba sanin shi acikin masu zuwa gidan su ba, Koda kuwa gurin mijin yar ta ne, bai daga cikin masu zuwa gidan,,, sam, Gashi kuma kaman nin sa sun nuna cewa kamar yana tare da lalura,,, Tafiya take yi a hankali, cikin dan shakku,kamar za,a kamata, Tana karasowa gab inda mutumin ke zaune sai mutumin ya mike tsaye da sauri ganin cewa gidan maryam ta dosa a lokacin, Cikin dan tsoro da kuma ladabi maryam ta dan duka kadan tace Baba ina wuni, ? Yace yauwa "ya ta lafiya kalau, Dan Allah ko gidan nan kike yan mata, ? Maryam dake dan ja baya baya kadan da kamar tace mai a,a sai dai ta daure tace mai eh a nan take, Hausar shi na nuna mata cewa mutumin ba pure hausa ba ne, Ya ce dan Allah yan mata ina son ki min iso a gurin mai gidan nan, Cikin mamaki Maryam ke kallon shi tace mai baya gari, Shiru taga mutumin yayi cikin damuwa yana mai dan ya mutse fuskan shi,,sai kuma taji duk yaba ta tausayi, Ita a zaton ta ko yazo maula ne irin yadda wasu masu kararen zuciya ke yi a wanan zamanin, Kaga mutum majiyi karfi amma sai ya kare bi gida jen masu hannu da shuni yana maula,. Mutumin ya katse maryam da cewa ko zan samu ganin hajiyar gidan don magana ce tazo dani mai muhin manci sosai Shiru Maryam tayi saidai gaskiya mutumi yabata tausayi sosai don ganin yanayin shi, Marayam ta fadi cikin ladabi barin shiga in fada mata, Bayan shigar ta da kaman yan mintina saiga Anty Dije ta leko sanye da hijabin ta,, Daga nisa kadan suka dan gaisa da mutumin sai kuma yar shiru tabiyo baya, Don Allah hajiya kiyi hakkuri pa don nasan cewa ba wai kin san,ni bane,,, Sunana Abdullsamad anan gari nake, ni dan uwan yaron dake yawan zuwa gidan nan ne, Watau Joseph,,,,, Daga Anty Dije har maryam dake ta kofa tsaye wace ta takawa yar uwar ta baya don gudun wani abu ya samay ta, Sai da suka dan kadu jin mutumin ya ambaci sunan Joseph, Jin haka yasa anty ta dan kara gyara tsayuwar ta tana mai cewa lafiya dai ko malam, Don a zaton su yazo masu da wani tashin hankali ne, a yadda suka gan shi,,, Yadan hada hannun shi guri daya ya nuna alamar cewa a,a babu komai gaskiya sai Alheri, Sai a lokacin anty dije tadan rage jin abinda take ji Sai yadan waiga kamar may son yin wani maganar ta,siri ko kuma mai muhin manci sosai, Hakan yaba anty damar gane cewa maganar da yake da ita kamar ta siri ce, Don haka ba bata lokaci ta dibi inda Maryam take tsaye tun farkon fitowar su tace maryam bude mai kofar falo tukun,,, Bayan an bude mai yadan shigo daga cikin ya zauna maryam takawo mai ruwa sanyi tare da dan abin tabawa, Ya dauki yar ledar ruwan goje water da ta aje mai ga plate ya dan tsosa kadan yace Alhamdullah, Nagode da wanan ruwan da kuka shayar dani Alkah yakara budi da daukaka, Daga Maryam har Anty sunji dadi sosai da wanan kalamin tashi, Hakan yakara basu damar sake jiki dashi don dama darrrr suke dashi saboda rashin sani ko da may yazo, Sai maryam taji kawai mutumin ya kwanta mata arai,, saboda kalaman bakin shi na alheri ne, Saboda ta lura cewa yana da addini atare da shi , Tsabar talauci ne kawai ke damun shi ya koma haka Wani irin mugun tausayin bawan Allah sukaji cikin lokaci guda, Maryam sai tunane take yi a ranta cewa,ashe daman wanan mutumin yana da yan uwa musulumai,,, Maganar bakon ne ya katse ta, da cewa, dan Allah kuyi hakuri nazo maku a bazata, tare da kuma bakon al,amari, Dama taimako da kuma shawara ne nakawo maku, akan cewa, Wanan yaron da ke zuwa gidan ku Joseph don Allah tunda har naku yazo daya dashi ina son ku dan tallafa mai , Nan da nan daga Anty har maryam suka dan kali junar su, Suna mamaki har may zasu iya tallafawa Joseph dashi su,,, Ai kuma sai mutumin yai shiru ,alamar maganar da zai furta tana da nauyi, Zuwa wani dan lokaci kamar mai tuna ne,,,,,, Can kuma sai yace, ku yi mai tayin musulunci a hankali pls, Yafadi cikin taushin murya, Duk da dai nasan cewa abune mawuyaci , amma nasan cewa zaku iya insha Allah,,,, Yakara fadi a raunane, cikin nuna damuwa sosai a fuskan shi, Shiru wurin yayi daga anty har Maryam dake tsaye kamar mai wancin gadin, yar uwar nata, Saida maryam takai zaune a gefen hannun kujera, dake kusa da ita, Saida Anty tadan nisa sai tadan daga kai zuwa kallon malam,Abdull samad tace A gaskiya malam kazo muna da mawuya cin abu amma da ace mai gida na yana gari ne kaga sai kuyi magana dashi ta yadda za,a fahinta, Katseta yayi dace wa ai koku da yake, zama daku a hankali zaku iya dan jan ra,ayin sa don dai yana da bukatar haka din Idan har kunyi la,akari da yadda rayuwan shi take,, Yakare zance shi da cewa ina fatan Allah ya baku sa,a Gaba dayan su alokaci guda suka ansa da Ameen ya Allah,,, Basu tashiba saida malam Abdullsamad ya basu labarin dalilin musuluntar shi, da kuma irin kalubalin da har gobe yake samu, daga mutanen shi nada,,,watau Christian, Yace musam man mahaifin Joseph da yafi kowa son kuntata mai, Saida duk kan su, suka tausaya ma halin da rayuwar ya shiga sukai mai fatan gamawa da duniya lafiya,, Anan yai masu sallama ,akan cewa idan maigidan yadawo zai zo sukara,tataunawa da shi akan zancen Joseph din In sha Allah,,,, Da zai tafi Anty Dije ta kawo dubu daya tabashi tace ya hau mashi zuwa gida Yai ta sa mata albarka yana ta godiya kamar wanda,taba wani abu mai yawa, Tun fitar wanan bawan Allah, duk sai jikin su,yai sanyi lokaci guda tankar, an aiko masu da wani labari, mai kashe jiki, duk su kai shiru zuwa wani dan lokaci,,, Kowa da abinda yake sakawa acikin zuciyar shi akan zancen,,,,,,,, Barci takeyi amma sai juyi takeyi kamar wace aka danne ta daga saman ta, Sai shure shure take yi da kafarta kamar mai bidan ceto, Zubur ta samu ta mike tana mai kumar ihu cikin wani irin karaji tace, JUSES crisis,,,, JOSEPH,,,,, tafadi da karfi tana mai dafe, kirjin ta, Guda guda take mai da numfashin ta sai wani irin zufa da takeyi kamar wace ke cikin ovon Wanan mafarki yana damun ta sosai yanzu, Har takai yanzu sam bata son tai barci asuba saboda , da wuya tai barci a wanan lokacin batai mafarkin nan ba, Still masu farin kayan da take gani suna kokari jan Joseph din cikin korarayen haki,, ko yaushe yau,ma su din ne dai tagani, suna ta kokarin jan shi,,,, Sai,dai ta yau mafarkin nata yadan bam,bamta dana kullun, Don dai yau,taga Joseph sosai a cikin mutanen,,,, Tana bin shi ta kamo shi amma sai ya kubce daga rikon da tai mai, shine mafarin wanan shure shuren da take ta yi, a lokacin da take mafarkin, Bible din ta dake gefe tadauko ta gyara daura dankwalin ta da kyau, nan ta fara jefo addu,oi da tasaba yi kamar kullun, har zuwa wani lokaci,,,, Koda gari ya waye ranan sai ya kasance mama choima ta kasa sake jikin ta sam bata walwala, yau, Duk abin duniya yadamay ta akan dan jikan na,ta Tsoro take ji don tasan cewa akwai abin da zai sami Joseph din, Saidai ta rasa ko may wanan mafarkin ke nufi, haka nan, Ejoma ta lura da cewa yau mama tana cikin wani yanayi don ko yaron Ejoma da take kokarin rike mata yau sam bata ko kalle shi ba, Inda take zaune tayi tagumi, Ejoma tazo tazauna gefen ta, A hankali Ejoma ke kallon mama, sai can tace, Mama yau may ke damun ki ne, wai ? da naga baki walwala, sam, Kamar kada ta fadawa Ejoma wanan maganar, Sai,dai kuma ta fara ba Ejoma labarin tun fara mafalkin nata akan Joseph din,,, Da irin yanayi da take ganin ahi a ciki yanzu,, Ejoma,tadan kwan,tar wa mama da hankali ta dan dafa kafadar mama kadan tace Kinsan cewa shi mutum ne mai harka da mutane kala,kala, mama, Don haka dole, yasa ko da yaushe kike ganin shi tare da irin wa yan nan mutane,, Har wani lokaci Ejoma da mama Choima suna zaune suna zancen duk akan Joseph din, Joseph din ne ya bugo masu waya yana tambayar lafiyar su, Anan mama tashiga tambayar shi labarin yaya yake can ya kuma aiyukan shi,, Inda yake kara mata karfin gwiwar da cewa yana tafe kwanan nan, Amma ita sam bata,yarda da zancen shi ba, don har yanzu idon ta na hasko mata masu fararen kayan da suka rike mai hannu suka wuce da shi tana ta kurma ihu,a daji,,,, Shiko Joseph yanzu yakai kusan wata, hudu a can Har kasar chaina, yake tare da wani abokin karatun shi, Cikin dan kankanin lokaci mr Sonny, da suke tare ya dan kara gwada mai wasu yan dabarun kasuwan ci, Allah da ikon shi ya kara daukaka shi sosai, ga harkan business, Ga harkokin shi na Nigeria su ma suna ci gaba, A, sannu yasamu ya kulla, a,laka da wayan nan mutanen suka yarda zasu zo Nigeria su kafa irin wanan masana,antar, Wanan harkan duk ya,samay shi da ga taimakon da hamshakin maikudi a kasar IBO yai mai hanya, abokin karatun shi Wanda tun kare karatun su shi yana can zaune yana harkokin shi, da turawa da chainawa, Mr Sonny shine ya basu sunar Joseph saboda yabawa da hankalin shi da yayi, Don tun a can da yasan halin Joseph sosai da rikon amana, Abin mamaki,Joseph nadawowa,da wanan harkan, Saiga shi ya dauki yaran hausawa cikin ma, aikatar company da aka bude Bunue,watau makurdi, wanda su yan kabilar su sam basu so hakan ba, A, bangaren su maryam da Anty dije kuwa, Tun bayan tafiyar wanan tsohon sai maganar tazauna ma maryam a zuciyar ta Tunane takeyi ta yadda zata fara aiwatar da wanan shirin kamar yadda aka basu shawara, su tallafa mai, Don haka tasawa zuciyar ta cewa zata bada nata gudun mawar amma ba tare da sanin kowa ba,, Don haka shiri na farko da tafara yi shi sayen sabon sim card na layin,MTN, Sabanin wanda kowa yasan ta dashi a da tana amfani dashi, A cikin wayar anty Dije ta samu nobar wayan shi tai serving a sim din ta,,, A wani dare bayan ta gama komai tana shirin kwanciya ne Sai zance malam Abdulsamad yafado mata arai, Tashi tayi tsam daga inda take kwance,ta dauko wayanta, Ta rasa may zata rubuta da farko,sai can wanan Sakon farko da tafara tuwa shine, Come to the light of life, islam,,,,, Joseph dake zaune yana searching din wasu kaya a cikin laptop din shi yaji sako ya shigo mai a wayar shi,, Kamar ya share kada ya karanta saidai ya mika hannun shi yadauko wayar, a hankali, Da niyar,yadan diba sakon yaci gaba da aikin shi, Sosai yai mamakin ganin wanan sakon awayar shi batare kuma da da sanin mai nobar ba,, Nan da nan duk wani abin da ke gaban shi ya dushe mai, Kafin wani lokaci idon shi ya kada yai jajir kamar yaci gauta ja, A hankali ya runtse idon shi, yana sauke numfashi a hankali, ya fida wani huci ta bakin shi, Tsayin lokaci babu abin da ya iya yi ko tunawa, wayar ya kara dauka ya diba sakon, Ahankali, maganar mahaifinshi ya fado mai a rai, Inda yake yawan ce mai hausawa basu da kyau, don wata rana zasu iya canza ka Joseph,, Sai kuma inda Mr Ema ke cewa kadaina yawo da yaran hausaw don basu da tabbas, Cikin wani irin yanayi ya aje wayan kamar mai tsoron wayar, na shi alokacin,,, Da kyat ya iya mikewa zuwa cikin bedroom din shi jikin shi,duk ba kwari, Duk da ya kwanta da ya runtse idon shi ba abinda yake gani sai wanan sakon na wayar shi, Come to the light of life, islam,,, Rintse idon shi ya karayi kamar wanda bai son tunawa da sakon, ,,,,,, Maryam wace ke zaune bakin dan matsakaicin gadon su ita da Issalam, Takai wani lokaci tana jiran replay din shi saidai taji shiru ba wani alamar da wani sako tafe, Haka ta hakkure ta kwanta tare da tunane kasadar da tayi na tura mai wanan irin sakon duk da tasan cewa ba wai zai gane cewa ita bace, Amma dai tasan cewa kasada ne haka din, don ina ruwan ta da addinin shi, Tsuki tayi gami da juyawa tana may ganin laifin kanta, dayin katsalandar da shiga harkan da ba nataba, Sim din tacire a hankali ta samu wani guri inda tasan cewa, ba mai taba ganin shi gurin, taboye A hankali taja bargon ta dake gefe aje, tai rufe jikinta da shi ta,na mai lumshe idon ta, Sai dai sam barci yaki daukar ta don tana tunane akan sakon da ta tura, May ye,wai, amfani abokan shi su jibrin da KB da bazasu iya fadakar da shi gaskiya ba, Tsuki tayi gami da kara juyawa ta wani gefe tanamai cewa Ina zasu iya fada mai gaskiya tunda suna samu kudin agurin shi a kai a kai, Wai may yasa mutane kudi ya rufe masu ido ne haka da yawa, Kudiba fa, ba kunya yadda suke rawan kafa akan ARNE, wanda suke darajawa da kiman,tawa saboda kudi,,, Shin wai basu san cewa shi kanshi yasan cewa sun fi shi daraja ba da kima mutunci, saboda hasken addinin su, yafi na shi,,,, Amma saboda kwadayi duk sun zubar da damar tasu, Kara jan bargon ta tayi ta lullube lif daga haka barci mai nauyi ya dauke ta, zuwa wata, nahiyar,,,,, A,A masuga ne zaune a office din shi yai tagumi da hannun shi, guda , Ba komai yake tunane ba sai wanan yariyar da yafara ji a, cikin zuciyar shi, Watau Maryam wace duk wani tsari da kuma diri da yake bukata ga mace tana dasu,, Kafin ya kai karshen tunanen shi yaji an turo kofan office din nashi, A hankali yadago kai da idon shi da suka dan sauya yanayi yana mai kallon kofar , Da sallamar ta ta,shigo office din cikin shigar atamfa, da dan hijabin ta mai kara mata kyau ko yaushe, A nutse take kamar kullun yau madai kamar ba sabo a tsakanin su har yanzu, A mutunce ta dan durkusa ta gaishe shi, sannan ta dan samu kujera guda ta zauna, Sai a lokacin A,A yadago ido ya zuba mata su kamar na yan mintina, A kunyace maryam ta kauda kanta daga kallon shi, saboda bazata iya jure kallon namiji ido da ido ba, Yar murmushi yayi har fararen hakoran shi suka dan baiyana fili, Magana yake yi mai kama da rada,maryam kina kokarin ki min illa a wani part na jikina, Cikin dan razana da dago idon ta,akaro nabiyu suka kara yin arba da juna, A,A yace yes, ba wai, ba gaskiya ce nafada, saboda duk second ina ganin ki a zuciya ta Maryam Cikin mamaki maryam tace mai malam ni kuma ? ta fadi cikin sanyin murya,, Kai yakada mata a hankali, yace akwai wata maryam ne nan a tare da ni, Ido ta dan kura mai sai kuma tai saurin kawar wa , azuciyar tako tace ban taba tsan manin cuta da ga gare ka ba malam, Ansar da yaba tane yasa ta gane cewa zancen zuci ya fito fili, Don ji tayi yace har abinda yafi haka zaki iya ji daga gare ni ai, Zan cena sam babu maganar cuta ko yaudara acikin ta, Gaba daya suka kurawa juna ido cikin dan mintina, Maryam ce tai saurin kawar da na ta idon again Saboda in badon a zaune take ba da zata iya faduwa don kaduwa, Sannu a hankali A,A masuga yaciga bada kafa gwaunatin shi a zuciyar maryam, Cikin jin kunya da kuma nauyi Maryam tai mai sallama daniyar wucewa yau ita kadai,, don dai wani irin nauyin malam din take ji yau,,,, Tafe suke ya na,takara kafa gwaunatin shi gare ta, ita ko har yanzu ta kasa gaskan ta zancen nashi a cikin ranta,,,, ZEEE. MAKAWA [2/20, 10:28 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Masoya novel din furen juji ina maku fatan alheri aduk inda kuke ina kara maku fatan gamawa da duniya lafiya , Rahama ,daukaka azurta,dacewa da alheri ubanginji Allah ya hada ku dashi, Don nasan cewa bawai novel din kuke kauna ba kishin addinin mu ta isalama yasa kuke kaunar novel din, fatan alheri gare ku ko yau she👏👏👏👏👏👏👏👏 Tsaye yake a cikin dakin shi yana daura agogon a hannun shi wanda ke mai masifar kyau aduk lokacin da ya makala agogo a hannun shi, Jerked din shi yadan aza saman wuyan shi, hannun shiguda ya rarimi yar Case din shi, da ita, A cikin sauri yake kokarin yin komai hakan kawai zai sa mutum yagane cewa yana da wani abu mai muhinmanci yau agaban shi, Da dan sauri sauri yake saukowa daga step din yana kokarin gyara tie din dake makale a wuyar shi, Tun bai karasa sauko wa ba Ejoma dake tsaye a bakin dinning table take mai wani irin kallo, Kofa yanufa don yau baiko tsaya zuwa gurin kakar shi ba, Brother, abinda Ejoma ta furta ke nan kamar yadda take kiran shi, where, are u going Your break fast is ready now, Tafada cikin yar shagwaba kamar yadda yan kabilar su keyi wa yayyen su, Dan tsayawa yayi, cak, Agogon shi yadiba ya dan ya mutsa fuskan shi kadan yace mata, Cikin dan sakin fuska sorry sister, i don't have time for dat pls,, Kai Ejoma ta kara dan langabewa tadauki cup tea ta,nufi inda yake tsaye har a lokacin yana kokarin gyara nicktie, din shi, Cup din tea din dake hannun ta tamika, mai tana cewa brother i beg drink dis ,even small now, O my god, Ejoma iam telling ,u now, dat iam, late, Ba yadda ya ita dole ya karba ya dan kurba tsa,tsaye, kadan kadan, Yamika mata cup din cikin sauri yabar falon don gudun kada Ejoma ta jawo mai wata matsalar kuma Yana fita Ejoma dake tsaye tadan bi bayan shi da kallo tana dan girgiza kanta,, Busy man ta furta, Ba laifi don yasa bakin nasu basu karaso ba, gurin da za ai taron, Wasu yan kasan Cameron da Guinea ne zasuyi wani dan meetings da su ta yadda zasu dinga tura masu mai acikin farashi mai sauki, Sai kuma kada watau ( Cotton) zasu yi harkan business din shi dasu, Sosai Joseph din ke jin dadin meeting din tare da bakin nasu saboda akwai abubuwan da ya fahinta so sai a fan,nin kasashen biyu,,, Tsawon wani lokaci suna wanan, taron har zuwa daidai da lokacin sallah a zuhur, Kawai sai mutum guda daga cikin su baki,ne so sai wulk da shi,wanda ke cikin shigar bakaken coth Tare da wani daya wanda shiko wasu kanan kaya yasa sun bala,in yi mashi kyau sosai, Mutumin farkon ne yafara daga hannun shi yadan kalli agogon hannu, wanda ke nuna karfe, daya da wani abu na rana, Mikewa yayi zubur yana mai ce ma sauran abokan meeting din I want to pray, Joseph da a,lokacin yake kokarin diba wasu takardun dake a gaban shi yai sauri daga kai ya kalli mutumin Wanda shi azaton shi tun farkon shigowar su yadauka dan bishon ne, Wai a,she muslumi ne, diban shi yakara konawa ga gudan da ke kojarin sance agogon hannun shi Kamar yadda yaga su KB na yawan yi idan zasu yi, alwala, Duk a cikin mamaki yadinga kallon su a zuciyar shi kuma cewa yayi, Ashe shi musulumi bawai dole ta kam ki wani hali zaka iya sheda shi ba ke nan kamar yadda yaga sauran, musullumai suna rike tasbaha ko kuma rawani ko sa tufafi mai nuna sheda, Kafin ya farga yana a cikin tunanen sai gani wa yan nan biyu dake gefen shi sun mike suma zuwa yin sallah, Ya kai wani lokaci yana ta al,ajabin wanan abin da yagani a tare da wa yan nan baki nasu, sosai, Wayar shi tai kara don haka yafita tadan waje kadan daga dakin taron,don,yar karba call din, Abakin wani daki dake gefen inda,suke taron yaga takalma mutane agurin, Sautin ladani sallah yaji har inda yake yana fadar Allahu,Akbar, Sami,al,llahu limal,hamd Kamar ance ya waiga hango su yayi still suna cikin shigar tufafin da Joseph ke tunanen zasu hanasu yin sallah, Can karshe yanufa ya ci gaba da maganar da yake yi, Har zuwa dawowar shi sun rarage sallah sun idar suna zaune suna lazimi, Ya zauna bada wani jimawa ba saiga su Aoudullah sun shigo duk kan su fuskan su cikin fara,a, Nan suka fara mikawa mutane hannu suna musabi,a da duk wanda ke gurin, Sau guda yadan daga kai ya kalle su yai saurin kawar da kan shi, Sai dai haka kawai ya kalli yan uwan shi Christian dake ta harkokin su cikin rashin damuwa,,,,,, A gajiye tafito daga dakin daukar lectures din din su yar jakar ta na sabale a kafadar ta, Tasan cewa A,A yana aji a lokacin don haka bata wahal da rayuwar ta zuwa office din shi, Saboda yanzu ma duk ta rage yawan zuwa gurin shi don guje wa shedan, A,kwai wani dan korido wanda zai sadaka da wata department namasu yin computer science, Iccen da ke gurin andan kawata shi da wasu kuherun kasa da akayi wa farin penti, Can ta nufa da niyar zuwa ta zauna, kafin lokacin shigar ta lecture yayi, Wata matashiryar buduwar ce zata dan girmay ma maryam kadan, Zaune take ta hada kai da gwiwa alamar a cikin tashin hankali ,take,don tayi zaune tayi tagumi, Gefen ta maryam ta zauna tare da fadin Bissimillahi, Hannu tasa acikin yar jakar ta tadauko wani dan bunch din digestive, biscuit, da wani dan lemon kwali, Gefen da yariyar data tarar a zaune tadan kalla karo na farko tunzuwan ta tazauna gurin, Mikawa yarinyar ledar biscuit din tayi tana mai mata Bissimillah, A hankali yariyar tadaga kai da idon ta da sukayi jawur, a lokacin, ta,dan girgiza wa Maryam kai alamar a,a, tafurta nagode, Sau guda maryam ta dan tauna biscuit din sai taji kawai bataji dadin yadda ta lura da cewa yarinyar na kokarin share hawayen ta da gefen gyalenta, Lafiya dai ko Maryam tai katsalandar din tambayar yarinyar, Wani kuka tasake lokaci guda tace wallahi yar uwa matsalar malam nan ne ke damuna ace mutane yan uwanka musullumai su dinga maka sheri, A hankali Maryam ta aje kwalin lemon da tafara dan zuka a lokacin ta mai da hanjalinta gun yarinyar, Yarinyar tace ni sabuwar zuwa ce a wanan school din, gashi na kusa kamalla duk wani abin da yakamata inyi amma gashi HOD din mu yaki samun hannu a takarda na wai bai yarda da results dina ba, Wani irin mugun tausayi yarinyar taba Maryam jin bakinta kawai tayi yana tambayar yarinyar wani department ne, Tace computer science, zubur Maryam ta mike ta kokarin gyara gyalen da tai rolling din kanta dashi, Shigar shi office ke nan yana kokarin dauko ruwa acikin dan karamin Fridge din dake office din, Da sallamar ta shigo office din sam bai zaci zuwanta yanzu ba don yasan cewa sai ta gama abin da takeyi takan zo su wuce gida, watarana ma sam baya ganin ta saidai suyi tayin waya, Ganin ta yanzu yasa yasan da matsala fuskanta ya dan kalla yaga damuwa fal acikinta, Daidai lokacin da yake zama yake cewa lafiya kuwa Maryam, Ido tadan tsura mai yau babu ko kiftawa, yai mamakin hakan sosai a, ranshi don yasan cewa ba halinta bane hakan, Zai yi magana sai yaji muryan tana cikin rauni tana magana,a hankali, Malam banaso sam, sunan ka, ya dinga fitowa daga cikin azzaluman malam makarantar nan, Masu kokarin kayarda ditan mutane, daga cigaban su, Kafin taci gaba yadaga mata hannu alamar ta tsayar da zancen ta hakana, Cikin mamaki yake tambayar ta komay ke faruwa da har tazo mai a haka,? Nan ta kwashe yarda sukayi da wanan yariyar ta fada mai, A, cikin mamaki yake tambayar cewa yaushe akai haka da shi,sam bai ma san zancen ba Can yace ina ita yarinya tana daga waje inji Maryam, Da sallama maryam suka dawo tare da wanan yarinya,,, Cikin ladabi tagaida malam din wanda ke dan rubutu a wani dan pepper,, Yadago kai yakali inda suke yana mai mika mata hannu alamar takawo takardun ta, dake hannun ta, Ba,bata lokaci taciro su daga cikin handabag din ta, ta mika mashi su, jiki na rawa, kamar zata fadi don tsoro, Tai mamaki kwarai da taga yasa mata hannu batare da bata lokacin komai ba cikin yan mintuna Ita ko yanzu kusan wata daya da rabi ke nan tana ta faman bin, ai, mata wanan aikin abu ya faskara, Sai gashi yau Allah yakawo mata shi a cikin sauki ta samu an mata, Yana gamawa yadago ido ya kalli yariyar yace mata kin taba gani na akan wanan takardan, Tace duk lokacin da nazo sai messenger ya ce min baka nan komaya yace ance bazan samu ba karshe ma sai ce min yayi ance takarduna basa yi wai,,,,,, Bayan fitowar su ne wanan yariyar ta rungumay Maryam tsam a jikin ta tana ta zuba godiya anan take sheda mata cewa sunan ta Safiya, Tundaga wanan ranan suka kulla friendship mai àkarfi a tsakanin su har takai in har guda baiga guda ba, bai jin dadi, Yau tsawon kwana biyu kenan Safiya bata shigo makaranta ba, Don haka Maryam tashiga cikin damuwa sosai, Nobar wayan ta takira wanda kwana biyu kenan nobar bata shiga koda takira sai ace is switch off, Yau kira guda Allah yasa nobar yashiga, batare da wani bata lokaci ba aka dauka a dayan bangaren, Nan take jin cewa ai safiya mahaifiyar tace bata da lafiya suna asibiti da ita, Maryam taima safiya alkawarin zuwa dubata, insha Allah, Sukayi sallama tare da aje wayan cikin nuna tausayi, Maryam ta fadawa Anty abinda yasamu mahaifiyar safiya,da ke asibiti kwance, Itama dai anty ta tausayawa safiya da mahaifiyar ta, Cikin wata raunaniyar murya tace wa anty idan tasamu time weekend zata tafi ta dibo maralafiyan, Anty Dije tace Allah yasa don dai ke ce da kanki kikayi wanan alkawarin don nasan cewa bazaki tafi ba, Cikin dan marairaice murya, Maryam tace, insha,Allah zan kokarta in tafi, ai saboda safiya nada kokari wlh,, Da dare suna zaune a harabar tsakar gidan su suna shan iska Saboda dauke wutan neper da akayi yau garin yai zafi, Sallama suka akofar shigowa gida, Maryam wace ke kwance saman wata tabar roba da suka baza tana karatu don tana da test a cikin satin nan,,,, Cikin mamaki gaba dayan su suke cewa muryan baba ne fa, Cikin farin cike duk suka mike suna tariyan shi, Wani tabarma aka dauko wa baba yazauna tare da jawo Isslam da Assalam zuwa jikin shi,,, Sun gaisa sosai da baba sai shiru yadan biyo baya, Baba yace wa Anty Dije yazo ne yadibi lafiyan su, da kuma zancen maryam, Maryam wace ke zaune gefe guda gaban ta yaba da damm, Nan baba yake tambayar Anty may ake ciki ne da zancen Anty Dije wace ke dan gefe tsugunne tadan kara gyara zaman ta tace wa baba, Baba maryam fa karatu takeyi yanzu dan Allah ba ba kayi hakkuri har tadan karasa sai ai zancen auren ta, Baba ya ce, a,a Dije banaki tanaki bane saidai kin san cewa yanzu mutane ba sui ma baya, Kin,ga gara tun inada rai muyi mata aure kada in mutu in barki da nauyi ke kadai, Maganar taso taba anty Dije dariya sai dai ta yar murmusa kawai tace Insha Allah baba kana da rai maryam zatayi aure kuma kaida kanka zaka aurar da abinka, Amma zancen cewa zaka tallafa min sa abinda zan aurar da ita don Allah baba ka daina wanan zance,, Allah zai hore min duk wani abu da za,ai mata, baba ya ce haba Dije ayi haka,? Da ki bari in saida yar shanun da nake kiwo sai in baki ki kara don kinga mahaifiyar ta nasan ba komai za,a samu a gurin ta ba tun da a kauye suke, Daga Anty har maryam saida tausayin dan tsohon ya kama su, Anty Dije tace cikun wasa baba kaje ka saida shanun ka kuci abinci da iyalin ka, Allah na nan zai rufa asiri insha Allah, Mudai fatan shine kai mata addua Allah yabata miji na gari, Ameen Ameen baba yafara fadi yana mai jerowa yqr diyar tashi dayake kauna aboye kuma take bashi tausayi kasan cewar ta ita kadai a gidan, Bayan tafiyan baba nan su ka zauna suna tausayin mahafin nasu mutun wanda baison hayaniya kuma bai shiga harkan kowa, Auren KB yataso sosai da ma so yake ya karasa ginar shi sai ata da zancen, Don haka yanzu da ya karasa ginan ya ta da zancen, Saboda yana bukatar yai azumin bana da matar sa, Saidai gidan matar sun dan kawo mashi tasa matsalar cewa basu shirya ba, Nan KB din yabude masu wuta babu sassautawa, cewa shi fa yana bukatar matar kafin watan ramadan, Maryam dake kitchen tanawa anty aikin abinci tanajin yadda KB ke fadawa wani wanda bata fahinci kowaye ba acikin waya, Saidai daga karshen zance taji KB din nacewa nifa gaskiya na kashe kudi masu yawa a wanan harkan, Sannu sanu taji yana rage tsauriñ masifar da yaketa zubawa a waya, da alamar wanda suke wayar ya dan lalashe shi ne, Cike da takaici maryam ke aikin ta tana sauraren kb wanda ke zaune a falo shida mijin anty dije, da ita anty dijen, Jin ya ambaci sunan Joseph yasa ta tuna dashi saboda da,dewan da yayi bai shi garin ba, Zancen tsohon nan yafado mata arai ganin cewa ga mijin antyn ta agari gashi bai zo ba akan zancen, A cikin hikima da dabara ta tunawa anty da zancen nan anty ta kwashe komai ta fadawa maigidan ta, Shiru yadan yi yana tunanen zance, Can yace wa matar shi kin san wanan wani babban al,amari ne, Don dai da wuya Joseph ya can za zuwa wani addini tunda har kikaga yakai war haka bai nuna wani alama ba, Don haka kawai kubar wanan zancen kada ku dauko min magana at last, Maryam dake sauraren bayan nin mijin yar nata sai taji wani haushin shi yakama ta, Bata san irin halin mijin yar uwar nata ba da rashin son tallafawa addini, Wanan ai taimako ne amna sai gashi yana kakaucewa, Batare da wani kwakwaran magana ba mijin yar nata yabar gari,wanda hakan yakona wa Maryam rai, Dadare bayan tagama komai ta sa wanan sim din nata na boye ta dauko tasa,a wayar ta, Tai rubutu kamar haka A TRUE BELIEVERS, BELIEVE IN ISLAM,,,,, ZEEEE MAKAWA,,,,,,,, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Tun Mr Ema yana fushi da dan shi kan laifin da yayi sai gashi yanzu shi da kan shi ke bukatan dan yazo gari, Saboda irin dadewawar da yayi bai shigo garin ba, A, gaskiya kuma baida time yanzu kamar da, da bai wani aiki mai yau, don yanzu ko kasar bai faye zama ba, Duk wanda yadade baiga Joseph ba idan ya gan shi yanzu yasan cewa akwai canji so sai, Yanzu ya zama mai dole ya shigo badon komai ba saidon kare mutuncin church din su, Church din su da ke fuskantar barazana daga sauran churches din dakw garin, Taro ne zasu yi nakasa mai girma wanda saboda hadin kai irin nasu duk inda mabiyi wanan church din yake dole ne yazo da jamar, sa, saboda da ci gaba, Yan churching su Joseph sun gano cewa ana so a zarta su daga wata kungiyar kirtawa, Don hakane suka hada wanan taron na ci gaban su, Shiri so sai Joseph yaiwa wanan tafiyar saboda irin dadewar da yayi bai shigo garin ba, Maman Choima da Ejoma da danta, sai shi Joseph din dake jan su da kan shi tun daga Lagos, Tanks god ya furta a hankali kamar yadda yasaba maganar shi cikin natsuwa,,, A,lokacin da yahango irin aikin da yaita turowa ana gyara masu gidan su, Ginan yayi mai sosai don tun daga nesa yahango ginan ya fada da anguwa sosai,, Baka jin komai a motar sai muryan wata mawakin IBO mai waken churches, Rabeca Gebrin, Joseph nason wakokin wanan mawakiyar mai zakin murya saboda iya fitar da baitoci da takeyi ga Jesus, A hankali shima yake marming din wakar inda kusan daidai da mawakiyar bakin su ke tafiya, "Keddo, "Edema yye Jesu, Na,belewawooo,,,, Shima bin wakae yakeyi yana dan dukar sitiyarin motar,tashi,, Kyawon motar kesa mutane na waiga wa don bakuwar motace da nobar Lagos, Mr Ema yai murna kwarai daga ganin dan nashi wanda sun kusa shekara guda bai,zo ba, gashi yai, wani irin fresh, Yazama full getle man, ya aje wani irin saje da yadan kewaye mai fuska gwanin sha,a wa, Duk Wanda ke gidan yau murna sukeyi da zuwan Joseph tare da su Granny, da Ejoma, Kamshi kakeji duk inda kabi kala,kala, a cikin gidan jen yan mabiya churching Catholic,, Shi kan shi Joseph yaji dadin yadda ya, samu mahaifin shi a cikin koshin lafiya,,, Inda mahaifin yake ya iso ya dafa kasa da hannu guda yana mai daga kafa guda ta baya,daidai saitin kafar mr Emanuel, Kan yaron nashi yadafa yana mai yi mai addu,a,acikin ki,rari,,,, Dan murmushi yayi yana mai mikewa cikin jindadi, samun blessing din ya yi daga mahaifin shi, Daga Maman Choima da Ejoma duk sun zo inda yake sun gaishe shi, Ya amsa ba yabo babu fallasa,tunda baida yadda,zai da halin dan shi wanda yasha warning din shi kan su,,, Bawani abinci Joseph yaci ba sosai don haka suka ci gaba da shirye shiryen su, Yau kam churchi ya yayi mugun cika makil da mabiya wanan akidar ta Catholics, Bukine sosai babu kama hannun yaro anan aka shirya wani kungiya, wanda zasu dinga bi kauyuka suna jan ra,ayin mutane da abubuwan duniya, Joseph na daya daga cikin wa yanda suka bada gudun mawar su don asai kayayyaki, da za,a rabawa kauyawa, dakuma masu bukata daga cikin su,,, Wani irin ihu church din yadauka bayan jin abinda sukatara har yafi abinda suke tsanmani samu da farki yawa, Wani dan gajeren mutum ne tsaye da lassifika yana cewa "PRESS THE LORD; Sai sauran su karba mai cikin murnan jin dadi suce "HALELOYA' Nan take masu kida sauka hau kada ganga duk kowa ya mike akafara wankan JESUS DEY HEAR, HE, DEY,,,,, Duk wurin yarude da wani irin ihu sai tafi kake ji, da rawa maza da mata,yara da manya,,,,,, A hankali yazamay jikin shi daga cikin su yana dan tabe kamae may zuwa yin wani abu, Sai alokacin ya zaro wayar shi daga cikkn aljihun shi yana ta kokarin bidan nobar waya, Bai tsaya ko ina ba sai gidan, su Ànty Dije, ta kofar gidan gidan ya tsaya yace ace yana wa Assalam sallama, Anty Dije bata gida maryam cs da yara kawai a gida suna kallo a falon gidan, Shigowar yaron da aika aiko kiran Assalam ne yadan sa su daga labuken falo, Maryam na zaune da waya a hannunta tun kusan minti ashirin suke waya da A,A, din ta, Sam bataji yaron ba har fitan Assalam din sai dai ganin shigowar Joseph da assalam tagani ya na rike gam da hannun shi, Muryarsa mai,taushi yai sallama da ita tankar musullumi, Tuni zuciyar maryam ta tsinke, don ta rasa da wani kallama zata ansa mai sallamar tashi, Mikewa tayi zaune daga kishingiden da take saman kujera, Ganin da yayi tadan dadirce yasa shi samun daya daga cikin kujerun falon yazauna Yana mai jawo Assalam zuwa jikin shi cikin nuna kulawa da kuma yar fara,a man,ne a fuskan shi,,,, Sannu da zuwa ta iya furtawa a lokacin A dakile ya amsa mata da yaiwa, saboda sanin halin miskilanci irin nata, Issalam dake zaune tun shigowar shi ta tashi cikin murna ta nufi gurin shi tana cewa Uncle sannu da zuwa, kamar yadda uwar su tace su dinga ce mai, Wani irin laulausar murmushi yasake mai yar sauti yajawo ta zuwa kusa dashi yana fadin, Wai, wai, wai Issin mama may aka baki haka kikai girman nan, Sai a lokacin Maryam tadan kalle shi a karo na farko tun shigowar shi falon, Cikin sauri takauda kai a zuciyar ta tana fadin Wa,subbahanallahill, Azeem, Saboda yada taga Joseph yakoma lokaci guda , Yazama wani irin, handsome guy, ,sai ka rantse kace ba,a kasar nan yake ba, Sanye yake da dinkin shadda sai shining shaddan keyi sky colour, Ga wani sarka da zakai ma kallo guda kagane cewa ta gold ce, Akawo ma ruwa tasamu bakin ta da iya furtawa a lokacin, Harara ya dan sakar mata ta gefen ido yace No ki barshi kawai, Sai yaci gaba da hiran da yakeyi da yaran suna ta kwasan dariya, don jin dadin kasancewa dashi, Wayan ta ta dauko taima antyn ta text cewa ga wanan kafirin mai zuwa yazo, Saiga Anty ta kira layin maryam din tana tambayar ta Joseph take nufin yazo ? Maryam tace eh shine, Mikewa Maryam tayi tana mai hada kayan wayoyin ta da kuma wani takarda da take dibawa, Ba,a dauki wani lokaci ba Anty Dije tadawo daga unguwar in da ta tafi karban, bashin ta, Da murna Anty Dije ta tari Joseph suna ta kwasan dariya , Maryam dake daki duk sai taji haushin Anty Dije don may zata dinga washe baki da kafiri, Sosai yake dan ba,Anty labarin irin abubuwan da suka dan faru dashi bayan wucewar shi, Maryam mamaki irin shakuwar su tankar yan uwa takeyi,, Don dai ko yan uwan su da suke mahaifi guda basu shaku da Anty kamar haka ba, Wanan dibgegen motar da ya aje a kofan gidan su Anty Dije yasa mutanen gari sanin cewa yashigo gari,. Kafin wani dan lokaci mutane sun farga da zuwan shi, Abokin Damo, Tsari, sai ga KB da jibrin su ma sun shigo garin, Abinda maryam bata so shi yadawo don kagin wani lokaci gidan su fam da yan zuwa maula, Don sun figane masu samay shi a gidan anty Dije bisaga gidan mahaifin shi, Dayake gab ake da afara azumin watan Ramadan, Kowa kagani kokarin wanan shirin yakeyi, sam shi da ba musullumi ba bai san cewa wanan lokacin ya gabato ba, Sai da wani dan uwan Jibrin yazo gurin Jibrin din neman taimakon abin da zai dan sai abinci,,, Dubu biyar Jibrin yaba mutumin yana mai cewa kayi hakuri akwai mutane da yawa, Mutumin ya juya yana zabga godiya,saboda dama duk tunane ya ishe shi, ta inda zai dan samu abin da zai fara sayen abinci kafin ai masu albashi,,,, Haba dai man wanan mutumin fa kamar cewa yayi yanason abinda zai sayi abinci azumi ko,? Joseph ne ke tambayar Jibrin din, Jibrin yace haka yace, sai Joseph yadan kada kan shi alamar takaici, Yo aiko sukarin azumi bazai sai masu ba, haba, haba man,,, Kiramin shi pls, Dubu hamsi yabawa mutumin nan ya rasa irin godiyar da zai ma Joseph don murna, Yau shigan safe yai ma gidan nasu Anty, Dije saboda yana son shan kunun gargajiya da kosai, Yana Sanye da farar T,shirt anrubuta agaban rigar, snow, da wani jan kala, Sai dogon wando mai kyau ruwan baki,wani farin agogo ya makala a hannun shi na D&G, Sai kafan shi dake saye da wani farin takalma rufafu masu kyau gani, Maryam ce Anty tasa ta gabatar mai da kunu wanda yasha kayan yaji sai kamshi ke tashi, Da kosai wanda shima yaji hadin kayan markade, da aka soya su tare, Aikin kullun yake yi waya, don ko zama yayi kafin ya tashi sai yayi waya da kusan mutum ba iyaka, Yana daga cikkn abinda yakesa shi zama a gidan anty in yana gari don yakan samu time din yin waya, Tunda tadoso wurin fuskan shi na kallon gefe bayan shi ne, Tana isowa yajuyo fuska a daure, tamau, yace dan Allah kawo min ruwa mai sanyi pls, Mikewa tayi bayan ta aje dan tire din da tadauko kayan karin a ciki, Wani harara ta,dan na masa, alamar kama raina ni,ke nan, I don't have your time don ni ba yar aikin ka bace, Azuci take tunanen ta fada ashe, har afili, ana jinta,,,,, Cikin rashin damuwa yace mata sorry pls just bear with me for sometimes, Da sauri maryam tabar falon cikin jin nauyi da kunya don sam batai tunanen maganar zai fito fili har yaji ba, Tun shigewar ta bata kara fitowa waje ba saboda nauyin da taji, Saidai tana jiwo hiran shi da Anty yana tambayar ta a gamay da azumi, Ramadan dake tafe, Cikin hikima yakewa Anty Dije tamabayoyi tana bashi ansa yadda yakamata, Maryam dake waje tana tunanen cewa anty zata sako mai zance addini aciki sai taji shiru,, Ba wani tambaya ne yakewa Anty Dije ba, illa abinda mai azumi ke bukata, yasamu idan yai azumi, Saboda azumin mu da nasu ba iri daya bane, don su daga sha biyun dare zuwa sha biyun rana suke azumin su,,, Bayan wanan maganar tasu da kamar kwana biyu, Basai ga kaya niki niki wata mota Peugeot mai budaden baya ta,o dasu , Sukace Anty Dije akace sukawo wa inji Joseph yace zai bugowa ya suyi magana shi yatafi, Abuja, A cikin wayane yake mata bayanin cewa ta rabawa mabukata da sukafi bukatar taimako, wa yan nan ka ,,, Sai kuma ga su gero da sauran kayan hatsi ankara kawowa, Nan akaita bawa mutane sadaka saboda ba wanda yasan ko daga ina ne kayan suka fito, Sai daga baya mutane suka fara ganewa cewa Joseph ne ya base taimakon, Har gida wani mutum yazo yasamu Anty Dije da masifa cewa don may zata yaudare shi ta bashi abin kafiri yai azumi dashi, Inda yake shiga banan yake shiga ba taso yatara mata mutane, Kafin ma yabar gurin saibmutane gungu,gungu sunzo abasu sadaka idan akwai (Dan Adam,) Unguwa unguwa yasa adinga dama kunu da sugar ana bawa almajirai sadaka, Allahu akbar nan zancen ya tadu a gari cewa ai ya musuluntane kawai a boye, Saiga shi magana har wurin mutanen su ya kai bayan sun bukaci yazo, Nan yabugo masu waya cikin bacin rai yana sheda masu cewa ba ruwan su da shi balle su sa mai ido a harkokin shi Shi yana yi ne "for god sake,, Don haka bawai su za su nuna mai ga wanda ya kamata ya ba, ba, Basu gane mai ba ganin cewa yawuce sanin su ko don haka dole suka sa mai ido da halin shi,,,, Irin abin da yakawo ma gidan su Anty Dije ya ce ta rabawa yan uwan tav abin ba,a cewa komai, Bakomai yasa yai haka ba don kawai yadda yaga ta kamanta mai gaskiya ga abubuwan kamar yadda yasa ayi,mai,,, Malam A,A ma ya yowa Maryam kayan shan,ruwa nagani na fada, Kamar su kayan tea manya gwagwani, millo, sugar eggs, butter, cooker oath, cornflakes, dasauran su kamar yadda akeyi wa mace wace zaka aura wanan sayayyan a kasar kwantagora, Maryam taji dadin wanan kayan da malam,A,A yakawo mata badon komai ba saidon dama tana kyamar na gurin Joseph, Duk da tasan cewa dole wata rana tayi amfani da dayadaga cikin abin da yakawo a gidan,,, Ansa lokacin bukin KB sallah da sati guda don haka abubuwa suka dan cabe w anty saboda tana cikin masu gudanar da tsarin bukin Duk da gidan amarya sun nuna cewa basu so asa masu Anty Dije acikin har kan su, Don a cewar su, suma za,su iya gudanar da komi da kan su, Don gani sukeyi cewa maganar Anty yan matasan ke kokarin bi,,,, Sun manta cewa mutunci na iya sa komai don dai ita sanadin dantane duk yajawo mata wanan badakalar,,,, ZEEE MAKAWA [2/20, 10:31 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Bakaji komai sai karan na,ura, dake ta shi cikin make,ken falon Wanda komai da ake bida na hafuwar falo ya hadu, Jin shirun da wurin yayi zakai tsan manin cewa ba kowa acikin gidan alokacin, A, hankali yake dan tafita saman walking exercise machine din shi yanayi yana goge dan zufan da ke tsiyayo mai a goshin da wuyan shi,,, Sanye yake da wani bakin wandon roba har kasa mai dan ratsin fari a gefe, sai, bakar singlet maikama da wondon wanda baida hannu, Wayan shi sake gefe guda ne tai kara a lokacin badon yaso ba yasauko dan daukar wayan Anty Dije yagani baro,baro a screm din wayan, shi, Yai mamaki kwarai da ganin wayar ta da sassafen nan don bata taba kiran shi irin haka ba ,, Asanin shi madai shine mai kiran Anty din indan har yana da bukatar magana da su,,, Yana goge zufan jikin shi yana kuma mamakin kiran da safe hakan ga, Jiran wayan yakeyi ya katse saiya kirata da kan shi don haka yakewa mutane da dama, Kiran farko Anty dije tadaga wayar anata bangaren, Cikin dassashiyar murya ta ke mai magana Joseph gamu asibiti da mutumin ka yau two days kenan, Cikin daga murya ya ce what, Assalam baida lafiya har two days ban sani ba, Tace wallahi muna ce ko abin baikai haka ba, shine, yasa ban fadama ba, Yanzu ma shike tace wa wai baigan ka ba shine yasa yana buga ma, Wai, May ke da munshine Anty, Anty tace yadawo daga school da zazzabi , Shine daga baya ya abin ya koma mai combustion, fever, Cikin matsanacin tsoro da firgici, ya furta O God, da sauki dai yanzu ko, Anty tace eh to yau dai abin bai buga mai ba, gaskiya, Assalam din ne akabawa wayan cikin dasssashiyar murya irin ta marasa lafiya yake cewa uncle, zan sha Keisha sweet, da apple juice, Wani iri Joseph din yaji a lokacin don yasan cewa yaron baida lafiya a yadda yaji muryan shi, cikin waya,. Joseph baisan cewa ya shaku da yaron ba sosai, sai yau din Don haka, yinin ranan haka yayi shi cikin rashin kuza,ri don ji,ya keyi kamar ace yana agarin shima, a,lokacin don yaga yanauin yaro,, Gashi yai ta kiran su amma nobar nasu baya shiga, Sai zuwa dare yasamu layin, nasu, yashiga nan yakara tambayar su ,lafiyan yaro aka ce mai da sauki,,, Jin haka yai tunane don yasa irin halin hausawa musullumai, duk irin halin da suke ciki sai suce ai da sauki,,, Don haka ya yanke shawaran tun da safe yakama hanya kawai, Don haka ya kwana dashirin tafiya, duk wani abinda zai bukata don tafiya yai ready din su, Karfe shidda na safe ya bar garin Lagos zuwa kwantagora batare da,ya fadawa kowa ba, cewa ga shi tafe, Ganin cewa tun jiya batai wanka ba yasa ta cewa maryam tazo ta zauna da yaron Ita zata tafi gida tadan watsa ma jikin ta ruwa ko zataji dadi, Lafiya lau suka rabu da Anty Dije, Assalam din na saman gado yana,dan wasa da wayan Anty, Saida zata wuce takarbi wayan a hannun shi, a, lokacin yaron yadan kai kanshi saman filo, Maryam da hankali ta ke ga wayar ta batasan cewa yaron na cikin wani hali ba,, Wani irin kakari tayi yaron nayi ashe hakoran shi ne ke hadewa, yana bada wani,irin kara Cikin matsana cin tsoro da firgici maryam ta mike tsaye, ,da gudu ta kwasa tai hanyar waje cikin rudewa, Karo tayi da mutum yana kokarin shigowa dakin, Kamar daga sama ta ganshi tsaye kofar dakin a lokacin , Cikin rude take kurma ihu tana ce mai ya mutu, tana nuna inda Assalam yake kwance cikin mawuyacin hali, Gurin gadon yayi da sauri, ya dago yaron dake ta faman karkadawa, Daukan shi ya yi din rudewa zuwa office din doctor, Maryam na bishi a baya cikin wani iri tashin hankali, Duk saurin da takeyi kamar mai gudu baisa ta cin masu ba, Karban yaron sukayi suka cewa Joseph ya fito waje, ya tsaya, Maryam na ganin yafito batare da yatmron ba takaraso da guda tana ce mai ya mutu ko ? Innalillahi wa,ina alaihi raj,un take ta na,natawa cikin tashin hankali, Waya ta dauko daga cikin yar pos din hannunta tana kokarin kiran layin Anty Dije, Joseph wanda tun fitowar shi yake jingine da bangon dakin likitan,. Fuskan shi murtuk, kamar bai taba farinciki ba, yana mai kallon sama, Ganin tana kokari kiran layin wayar, Anty Dije ne yasa shi yi mata magana akaro na farko tun zuwan shi, Yace "pls don't call dem,, Wani kallo tai mai na baka da hankali, Daurewa yayi cikin jin haushi yace may zaki ce masu, Mamakin tambayar da yai mata tayi amma cikin dakewa , Tace in fada masu cewa yarasu, mana, Ido yazoro waje yace waya fada maki cewa ya rasu da zaki fada masu, Cikin mamaki take kallonshi don sam bata fahince shiba saboda rudewan da tayi, Fuskan shi a,daure yace mata suna dibashi ne Shiyasa na fito nan gurin har su gama aikin su,tukun, Wani irin ajiyar zuciya mai sauti maryam tasake tana mai furta Alhamdullah, Kafin wanin su yakara wani magana a,ka turo kofan wata yar nurse ce ta miko mai wani takarda tace ance kayi sauri ka sayo wanan, Cikin sauri Joseph ya wuce sayen maganin sai a lokacin maryam dake tsaye tun dazu cikin tashin hankali takai zaune saman wasu kuherun karfe da akajera akofar dakin likitan, Jafin yadawo aka fito da yaron zuwa dakin da yake da farko saida da alamar barci yake yi, Da Joseph zai dawo saigashi da kayan tea manya,manya gwangwani da kuma kayan shaye shaye, Nan ya zube kayan yadan je bakin gafo gurin yaron yadan dade tsaye yana kallon shi sanan yadan juya inda maryam take yana ce mata, Idan ya tashi ki hada mai tea mai kauri pls sai a bashi maganin nan, Zadu dawo zuwa dare sukara mai allura, amma dan Allah ku bashi tea ko kunu yasaha, sosai pls, Daga nan ya juya yabar dakin cikin tafiyar shi ma kama da ta yanga, Sai a lokacin maryam ta nisa tana mai kara mamaki da irin rayuwar wanan mutunin, Allah ya sa yagane gaskiya tace daidai lokacin da tamike ta dan fara gyara kayan da suka wawa,tse adakin,,,, Sallah tai haraman yi don har lokaci yadan gwauta, bata samu yi ba saboda rudewa,,, Sai zuwa tara na dare Anty Dije tadawo inda tasamu Maryam zaune gab da Assalam ta kura mai ido, Tunda tashigo dakin hankalin ta, na gurin su don yadda taga Maryam din a lokacin, Kayan da tashigo dashi a hannunta taje tana tambayar Maryam maynee, halan naga kin wani kura mai ido Maimakon Maryam tai magana sai kawai tasa kuka wi,wi,wi, A rane anty ke kara tambarya ta wai may akayi, Kuka yaci karfinta takasa magana,balle tai mata bayani, Jin anturo kofan dakin yasa Anty waigawa don taga kowaye yashigo, Joseph tagani yana sagale da yar jarket din shi a kafadar shi,. Cikin mamaki Anty Dije kallon shi sai tambayar shi,take tambayar shi yaushe iso, Yai yar gajerar murmushi yana kojarin karasawa inda Assalam yake kwance, Saida yakai bakin gadon yadan taba jikin yaron yaji da sanyi babu zafi kamar dazu,, Sanan yadan juyo yana gaisawa da Anty dijen, sai alokacin ne ya jai kallon shi ga Maryam wace ke ta faman sharar kwalla,, Ido yadan zuba mata nadan second, sai yakawar da kanshi daga gareta da sauri, Azuciyar shi yace dazun ma dayaron ya shiga conscious, batai kuka haka basai yanzu, Gefen gadon da yaron yake yadan samu gefen bakin gafon yadan zauna Nan suka fara hira yadda abin yafarawa yaron tun farko, Yace likita yace, harda typhoid, da kuma malaria ke damun shi, Maryam wace ta dauro alwalar sallah isha,i, tazo tada sallah duk alokacin suna ta maganar assalam din, Bayan tabidar ne Anty Dije ke cewa ki hada wanan kayan ki sauri ki je maryam kin san cewa issalam bata yarda dakowa in bake tagani ba Ga Joseph nan sai ya sauke min ke idan zai wuce, Gaban maryam ne ya fadi a lokacin don ita sam bata son wani alaka da zai hadata da shi,, Joseph tashi katafi ka huta ka debo gajiyar hanya, Anty yatafi kawai zan kira a kaini, yanzu, Anty dije tace Maryam ko da na bargida Issalam fa taki zuwa gidan su Salma, Da dabara nasamu nakai tacan nasan cewa yanzu haka tana can tana masu rigima Maryam zatai magana anty tace don Allah tashi ya sauke ki kada dare yakara yi, Wayan maryam din ne yai kara aloacin cikin murya mai shakewa ta ce, Assalamu Alaikum, Ido Joseph na akan ta don ya nason subar asibitin don yaje gida kafin maihaifin shi yashiga barci, Cikin shagwaba taje cewa gata nan zatabar asibitin zuwa gida yanzu, Tunda suka fara hanya ba wanda yai wa dan uwa magana Sai shine ma yai dan magana cewa ta danyi hakkuri yasai wani abu a kingays super market, Batare da yaji maitace ba yabude motar yashige abinshi, Kara kiranta A,A yakarayi a karo na biyu yana maice mata yana son ya wuce don badadewa zaiyi ba, Gashi Joseph kuma yasa security lock ya kulle motar don kada sanyi A,C ya rage, Batare da ta ganshi tafe ba. Dan guntun tsuki tayi daidai lokacin da yabude motar zai shigo,,, Ledoji ne birjit a hannuwar shi yazube su a gefen shi, Suna karasawa A,A, natada motar shi daniyar zai wuce abin shi, Ganin su ya sa yadan dakata sai dai bai san kowakeda qanan dirkekiyar motar ba haka, A hankali ta sauko daga motar daidai lokacin da shi kuma yafara tatara ledojin da yasiyo a super market yana kokarin bude kofar gefen shi,,,,, Cikin rawan jiki ta take saurin fita don gudun bacin ran A,A din gareta, Dan ma,kullin gidan da Anty ta bata dazata wuto take kokarin daukowa daga cikin pos din ta, Joseph yagane cewa hankalinta na gurin mai motar dake tsaye ya kun,na dim,light din motar, Da kanshi ya je har bakin kofar gidan yakarbi dan makullin daga hannunta ya bude gidan, Saida yakai duk kayan da suka dawo dashi daga asibiti zuwa cikin gidan, Maryam wace har lokacin ta gurin mai motar tadan rankwafa suna magana dashi Ganin cewa ba,ta,daniya barin gurin mai motar yai mata bayani cewa ga kaya nan tabawa Issilam Yasa shi tada motar shi yana mai yi muzu horn yai tafiyar shi, Maryam wace alokacin take cewa A,A, ya daina hadata da kafiri Arne, Yaga tashin motar shi nan yadan mata dariya cikin barkwanci yake ce mata yau dai na hana shi tsaya wa, Maryan wace ranta yakai kololowat baci ta wuce zuwa ciki batare da ta,tsaya yi mai saida safe ba, Shiko A,A da gangan yake mata wanan wasan don yasan cewa tayi hating din Joseph din, Tun zuwan shi bai hutaba akan ciwon Assalam don duk wani zirga,zirga da sayen magani yakan shi tun zuwan shi Da har yana cewa zai dauke yaron zuwa Abuja, Turkish hospital, Saiga shi yaji sauki sosai kamar bashi bane mai ciwo da duk yatayar wa mutane a hankali, Kuyi hakkuri pls ba yawa yau ZEEE MAKAWA [2/20, 10:35 PM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Wanan watan Azumin haka su,kayi shi rabi badadi saboda ciwon Assalam, Don bawanda yasa yaron zai tashi, amna sai gashi yasamu sauki, Joseph duk hankalin shi ya tashi zaka dauka wani babbane ko dan uwan shi baida lafiya, haka, Da kan shi yake zuwa yai wa Assalam komai daga wanka har shan magani da cin abinci, Wanan abin yakara sa shakuwa sosai tsakanin Joseph da mutanen gidan, Don ba wanda ya isa yasa Assalam yin wani abu in ba Joseph ya,zo ba Duk yadda kayi yaci abu baya ci inba Joseph ya,zo ba sai,kaga jikin shi har dan rawa yakeyi, Wanan sabon nasu yana bawa kowa mamaki musan ma idan kaga yadda,sukeyi, Yau ko da ya shi go sun gama abinci don da, wuri suke fara aikin girke, girken su na azumi don gudun makara, Shimkafa da miya duk maryam taga har ta,zuba acikin cooler wanda har asuba yana da zafin shi, Don haka ta saurin zuwa yin sallah la,asar, sai jin muryan Anty tayi tana fadin kawo wa su Joseph abincin su, Ànty sallah zan yi tukun don nayi alwala , Kifara kawo masu mana kafin kiyi sallah, Sai jin maganar maryam tayi wani iri, may anty nata ke nufi da fadar haka, Amma sai tani tana cewa kin san halin Assalam yana iya cewa bazai ci ba sai wani abin kwadai, Azuciyar maryam ta ce, watau ita don Dan ta take son yin komai akan wanan Arnen Muryan Joseph taji yans cewa "No, tabar shi kawai bana jin yunwa, Assalam kuma fruit zan bashi ya sha,. So, abar ta tayi sallah ta, kawai fitama zamuyi yau, mu dan yawata cikin gari Ya kare zancen yana mai mikawa Assalam hannu, Tun bayan fitan su gidan bayan maryam takare sallah sai ta share Anty kawai alamar tayi fushi,,, Basu dawo ba sai bayan shan ruwa daidai lokacin da har da yaya Illiya most jin Anty Dije yana gida don shima yadawo saboda ciwon Assalam din, tun kwana biyu da suka wuce, Maryam na,ganin shigowar su takara tamke fuskan ta don gudun, kara wahal da ita kan kafiri, Juice din subo da kankana da akayi mai sanyi yadan kurba, Daidai lokacin da yaya Illiya ke cewa Maryam, ke bazaki zo ki yi buda bakin ba A,a ba yanzu zan ci ba inji maryam take cewa mijin yar nata, da yaji tausayin ta a, lokacin duk da bawai yafaye damuwa da al,marin ta bane a gidan, Don tun tana yarinya bai damu da mata wasu abubuwa ba a matsayinta na kaunar matashi wace ke zama da su, Amma ganin watan Azumi ne ga kuma aiki, yai mata yawa har yadan ji tausayin ta ya,kamashi,, Maryam ko tana cewa ba yanzu ba ta daga idon ta daniyar wucewa sai ki suka hada ido da Joseph, Wanda ke kurban juice din dake hannun shi a hankali Ga sanyi ga kuma kamshin dadi na tashi daga cikin juice din, Suna hada ido tai wani daure fuska, kamar zata fashe, a lokacin, A, hankali ya furta cewa may yasa ba,zaki ci abinci Bayan kin yi azumi kada kijawa kan ki matsalar ulcer fa, Maryam tadan kauda kai gefe guda ta tsuke fuska tace, tace haka kawai, Tana duke tana kokarin ajewa mijin yar ta vegetable din data soya mai, Can yai dan shiru ga mamakin maryam sai kuma ta tsinci muryan shi yana cewa amma da ko tea ne ki dan sha don ki walwale hajin ki, ko, ? Tace ko banci ba yanzu, ba,abin da zai samay don nasaba da hakan,, Ànty Dije wace tun farkon zancen tajin abinda kewa kana kuma tasan cewa maryam tun rana fushi takeyi da ita, Anty tace dama kun bar ta tunda tace ba,za,taci ba ,bataci din, ne kawai, Yaya illiya yakalli matar shi yace kina nufincewa, idan anyi buda baki batayi a lokacin ko may, Anty Dije tace, a,a yau dai ne takejin hakan , saboda haka duk zancen da zakuyi mata bazataci ba tunda tace a,a, Yaya illiya yaidan murmushi yace kin,san dai abin da kikai mata yau din ne, Tace fushin da ba wani dalili takeyi kawai tunda rana, Dariya mijin Antyn ta yadinga mata, yana mata ba,a cikin zolaya, Daga haka sukaci gaba da cin abincin su sai kamshi girki ke tashi duk ya cika gurin, Daidai zata shiga daki wayar ta yai kara, cikin wani irin zakin murya tace Assalamu, Alaikum, Daga haka tashige abinta daki batare da kowa yakara jin may tace ba Sai bayan kamar minti goma sha lokacin har anfara kiraye kirayen sallahn isha,i, wasu gurare, Sai gata cikin wani katon hijab, tace ma Anty Dije, ciki , ciki, Anty zandan fita nan bakin kifar gida indawo,, Anty dije tace ana shirin yin sallah zaki fita, Shi bakon wani iri ne daba zai tsaya har a idar da sallah ba, Takarashe da cewa kada ki dade fa maryam, Maryam tafita abinta batare da ta,tsaya koda ansawa ba, Ankai kamar minti goma sai gata tadawo dauke da leda dakaya ciki ni,ki,niki, A inda suke ta dangware ledar yaya illiya dake alwala alokacin yace, a,a a gashi ko dan saurayin harda gudun mawar leda buda baki ya kawo muna, Abin mamaki nan yaya illiya yai alwala yabar Joseph zaune suna hira da Assalam da Issalam, Maryam wace itama dai sallah take a lokacin tana bin wani massallacin dake kusa dasu,jam,i, Bayan tahiya ansallamay tadan fakaici idon mutane ta tura sakon ta kamar kullun, Copy D Wright Things From D Wright Peoples,,,, Jin sakon yashigo mai cikin mamaki duk daga Anty har Maryam wace a lokacin sun fara Asham, sam baikawo cewa daga gidan bane, don dama bai taba tsan manin haka ba daga gurin su, Tana sallah amma hankalinta na gurin su don jin subar hira yayi shiru, Abinda maryam ta kula dashi shi ne undaga wanan lokacin duk jikin shi yai sanyi sosai Don yar hiran da sukeyi ma da yaran yadaina yanzu, sai yar shirun da yayi, Suna idar da sallah suka gaisa dashi da Anty, Maryam na,daki ita tafito suka gaisa, da Joseph Kullun irin ladabin yarinyar nadaure mai kai gata kuma da bahagon hali, Wanda bakowane zai gane ko may take ciki ba sai wanda yasan ta sosai, Saboda ganin farkon ka da ita zaka gane cewa miskilace ta karshe, Bai wani dade ba yacewa Anty Dije zai tafi, don yana son yaga wani, Maryam da tasan cewa baya cikin hayacin shi sai murmushi tayi, kawai yasamu ya tafi fa kyat don Assalam yace sai sukara fita yawo,,, Yana fita gidan maryam ta kasa yin hakkuri tadan kalli Antyn ta tace, Wai Anty shi wanan kato da shi baya jin kunya Kowa na sallah yana zaune sai wasa da yara baiko jin wani iri, aran shi, Da mamaki Anty ta kalle ta tace kunyan may zai ji maryam Runda shi ganima yakeyi ai yafi mu kama hanyar gaskiya, Ido maryam tadan fitar waje don mamaki tace a hakan sai shirmay kawai, taya ,zaiga yafi kama gaskiya? Bayan yana sane duk time din sallah sai mun tashi munyi sallah Sabanin su daga Lahadi sai Lahadi kuma ba wanin abinda za,a taru gabadaya a bautawa Allah dashi kamar yadda musullumai A kullun sai sun hadu sunyi sallah a guri guda sau biyar a rana, Haja kuma ranan jumma,a tankar idi ce agurin mumuni, don kowa na donkin samun wanan falalar da ke cikin ta, Ga Azumi da mukeyi gaba daya babu wargantawa a cikin ta don har da yara da azumin bai wajabta akansu ba, suna kokarin ganin sun samu wanan falalar, Anty Dije tace, ke kikasan wanan Maryam keda Allah yakebo daga ciki, Nidai har kullun ina mai mashi addu,an Allah yasa yagane gaskiya, yadawo hanya Gashi da hali msi kyau tankar wani mumuni, nikai ina kokarin jan shi a jikine, Ko Allah zai sa yagane gaskiya yadawo hanya, don kinga duk zagin da mutane ke min akan shi wallahi duk ina ji Nidai nasan cewa kokari nakeyi inga ya kubto daga bata, yadawo daidai, Allah ne ya hadamu dashi shikuma yasan dalilin kawo munashi anan, Mutun nawa ke cikin garin nan amma baidamu dasu ba sai mu nan, Shiyasa nake kokarin ganin ko ke kin daina masa wanan mugun hattaran dakike masa wallahi, hakan baidace ba sam, Kamata yayi muyi takokarin lurar dashi hanya mafifici cikin hikima, Chokalin dake hannun ta zata zuba shimkafa tadan aje a plate, Ta,dan turo bakinta ga ba kamar mai shirin kuka tace, Wallah Anty haka kawai nidai banson lamarin wanan mutumin, arayuwa na, Bashi ba suk wani kafiri wallahi haushin sa nake ji ni sam bana son alaka dasu, Dan bugu Anty takai mata abaya cikin wasa tace aiko wallahi ki bari don haka baida kyau,,,,, Shiko Joseph tin da Asuba yabar gari, yanufi makardi, don ganin wani abokin kasuwan cin shi,,, Kwanan shi biyu a can yasamu takardun da yatafi karba anan ne, yadawo Lagos Ya,nadawowa yasa mu gurin sanar su ana rikici akan farashin mai da suke son su karawa kudi, Don haka tunda safe ya shiriya tafi depot din nasu ,saidai duk security ne agurin, tako ina suna patrol, Duk yadda yaso yashiga hakan bai samu ba kuma ga motocin su da yawa aciki harda mutanen shi, Daga wajen dayake ne ya lura da cewa akwai yan batagari ake son tada fitinar tayi girma agurin Har yatada mota don yabar gurin sai ganin yayi wasu masu alamar yan Ejebo sun ke,waye wani dan musullumi ba haushe suna kokarin halaka shi,,,, Cikin wani irin ribas Joseph yai cikin su da karfin Allah ya bude gefen shi yana cewa mutumin yashigo Shi ma mutu yagane nufin Joseph din yafada motar da karfi ya fisgi motar shi tare da mutumin sukabar gurin, A jamian tsaro suka isu suka tarwatsa taron mutanen da harbi na gaskiya, Don gwaunati tabado dokar duk wanda yatada fitina a harbe shi, Sai da sukai nisa da gurin sosai, san,nan daga shi har mutumin sukayi ajiyar zuciya a lokaci guda, Gidan shi ya wuce da mutumin cikin tashin hankali, suka isa ganin shi tare da bahaushe yasa kowa nagidan yin mamaki, Wanan labarin tashin hankali duk ya karade kasa da kewaye cewa ana tashin hankali, a depot din Lagos Hankali mutane da dama saida ya tashi saboda, jin cewa ana ta kashe,kashen mutane a gurin, Wanan labarin har su Anty Dije sunji shi sanin cewa Joseph a gurin yake harkokin shi, Nan da nan anty tasa kudi a layin ta, takira Joseph sai taji ance switch, up, Hakalin su Anty duk yatashi tana takira bai shiga, duk nobibin shi dake gareta, A kashe suke ba ita kadai ba har su KB saida sika dinga kiranshi wayar bata shi, Shiko Joseph yaman ta cewa, ya kashe wayar shi tunda safe da zai shi depot din, Sai zuwa yamma ya tuna cewa bai, kunna wayar shi ba tun safe , A folon gidan nashi suke gaba dayan, su, suna kallo a, TV abinda ke faru a gurin live, ake gani,,, Duk wanda ya san Joseph hakalin shi a tashe yake, alokacin saboda rashin jinshi da,ba,yi ba, Yana tunawa ya kunna wayar aiko nan take kiran jama,a yadinga shigowa, Nan mahaifin shi yace mai yabaro garin ya nufo Arewa, Murmushi Joseph din yayi alokacin July n bayanin mahaifin nashi yace ai shi yana gida abin bai ritsa dashi ba saboda tafiyan dayayi zuwa markudi, Sun kai wani lokaci suna waya, da Anty Dije inda yasa aka bashi, kowan su yai waya amma banda maryam , Wace kamar bata masan abinda ke faruwa a gurin ba, Anty Dije ce takau da zargin da ce mai ga maryam zata gaishe shi, Mika wa maryam din wayar tayi batare da jiran ansar ta, ba, Cikin yar siririyar murya tace hello, Ya amsa mata ta bangaren shi da ce ya kuke yagida ya yara, Nagode fa, nagode kwarai, Batare da tace komai ba saidai karshe tace Allah y tsare, Duk wayan da yakeyi da hausa maman Chioma idon ta na kafe ga Joseph tana mamaki yaushe ya iya hausa haka Dasuwa kuma yake waya haka cikin jin dadi kamar yan uwan shi, Gefe tasamu Ejoma tana tambayar ta dasuwa Joseph ke waya haka, Cikin har shen hausa Ejoma tace gaskiya tana ganin kila abokan sanar shi ce daga kasar hausa suke mai barka da arziki, Tadan waiga kadan tacewa Ejoma tana jin tsoron kar maganar da baban Joseph ke fadi gamay da hausa ya zama gaskiya, Don kada Joseph yai hurda dasu ita sam bata ra,ayin haka gaskiya saboda basu da kyau, Tana fadi tana wani girgiza yatsan hannnunta, Sai bayan kwana biyar Joseph yasallami wanan bawan Allah yasa aka kaishi gida, tare da dan abin tabawa,,,,,, ZEEE MAKAWA [2/21, 9:09 AM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, Ganin haka da mahaifin Joseph yayi kuma yasan cewa Joseph din sanane, a gurin ya sa shi matsa mai sai yazo gida, Inda yake kwantagora, saboda idan yana kusa dasu hankalin su ,zaifi kwanci, Joseph da yaga cewa baban nashi ya matsa mai sai kawai ya shirya tare da duk wani wanda ke gidan suka koma Enugu da zama, Saboda can ma akwai business din da suke yi sosai a shigowa dashi mu san man da har yanzu yana kokari wurin ganin sana,ar mahaifin shi tana ci gaba, Yau ya kasance ranan sunday sai ya shirya tare da su mama da Ejoma wace ke dauke da dan karamin dan ta wanda suke kira da Jecob, Irin church din su da suke zuwa wan da aduk cikin churches yafi karfi da kuma yawan manyan mabiya, Musan man ma yan kabilar IBO sunfi yarda da wanan church din saboda da kasa shen,turawa suke hurda su, Duk wani tallafi da kuma koyarwan churches daga kasan turai ake kawo masu dauki,, Shigan couth baka da shirt din ciki, light blue, sai bakaken takalma, agogon shi na yau ta company Rolex, ce daure a hannun shi mai ruwan gold, Itama maman Choima watau kakan shi tana saye da wani farin lace mai duwatsu, Ejoma buje da riga ta sa iya gwiwar ta wanda ke nuna cewa ita din har yanzu ba macen aure bace, Don in matar aure ce zata sa zani ko wani kayan da zai dan sauka mata har kasa kadan,. Samuel kanin shi yana tare da su alokacin shi a shigar wasu kayan maz masu tsada irin na samari, Bayan yan baya nai da sauran addu,oi, da aka gabatar a church din sai kawai wani sabon zance yazo Wani pastor mai wata katuwa far riga anmata alamar cross da jan kyale, Ga wani babban hula da yasa akan shi yana rataye da wani katon,chasbi, a quyan shi, Wanan pastor ganin shi yana nufin wani babban sako zai gabatar, Don haka sai kowa ya natsu don sauraron shi aji may za,a gabatar, Bayan gaisuwa da kuma nuna yabo gare su, sai ya fara mika sakon shi, akan cewa har yanzu mutanen su suna yawan sakaci a kasan nan, Don gashi har population din muslim ya nunka nasu kusan kashi saba,in da biyar, Wanan ya nuna cewa, za, nan gaba idan basuyi hankali ba kasan zai koma duk na musulumai zalla, Su diba suga ni daga cikin su wasu suna barin akidar kwarai ta YESU, Al, MASIHU, suna komawa cikin isalama, Daga can wani mai zakin murya cikin masu sauraron pastor ya amsa da fadin JESUS CRISIS,,, Pastor yace yes gaskiyane wasun su suna barin wanan Christianity din suna komawa isalama, Don haka suyi kokari suga cewa duk wanda wani nashi ya koma cikin musulunci, sun bi duk hanyar da yadace su dawo dashi, Tunda musuluman da suke komawa gurin su basu iya tallafa masu gurin ganin sun ci gaba, Don haka da wanda ya koma da mawanda acikin isalama yake , kofa a bude take don basu gudun mawa wanda zai jawo hankalin su zuwa ga Christianity don ganin cewa takara ci gaba da bun kasa, Wata matashi mai wasu kaya blue ta amsa da babban murya tace HELLO ,LUYA,,,, Sauran ma suka amsa mata da makamancin abinda tace, Pastor yacigaba da fadin, akwai kasa,shen duniya da dama inda Christian suka kai yaran su mata don su musulunta su haihu, su Sai duk church din yadauki guna guni jin wanan maganar da pastor yayi cewa sun aura ma diyan su musulmai, Pastor yai yar gyaran murya don kowa ya samu natsuwa alokacin, do su fahince shi, Bayan kowa yana tsu sai yace su wa yan nan yara nasu bawai musuluntar gaskiya sukayi ba, Sunyi shine da wata manufa ta inda indan sun haifi yara dole yaran zasu dan kawo nasu akidar Christian acikin al,adun musulmai, HALLELUYA,,, inji wani katon arne yafadi hakana don jin fasan han da shugaban nin su sukayi, Guri ya rude da murna da tafi wasu harda buga gangan churching sukayi, Pastor yadan sa akayi shiru nan yace now,over to you, people's, Sai kowa yai shiru, sai yace yakamata duk wani mai saida sana,a wanda za,shigo dashi musanman a, Arewa cin Nigeria, to yakamata ya san abin yi aciki, Kamar su manja, lemon, gari, da sauran su, Dole su ma su san hanyar dazasubi su cutawa hausawa don suga cewa, an rage yawan musulumai Ko kuma su gurbata masu addinin su, sudinga hada abinda suka san cewa baida kyau musulmi yaci, Su zuba aciki don gurbata musulunci nan gaba , Su tura yaran su aiki a gidajen musulmai don su gurbata tarbiyan diyan su,kanana, da cutar da mazajen su da shayar da su guba gaba dayan su,,, Wata daga cikin su tamike tana cewa Sir, akwai yan uwan mu sosai acan Arewan suna zama har mada christoci, hausawa mazauna arewa, Idan sun saye fa suma, acikin rashin sani, Yar murmushi yati yace dole ai akwai matakin da suka dauka kafin su aiwatar da hakan, Yace zasu sa gamai tsada ga mai araha dole kowa yasan hausawa da son banza, Mai arahn ce zasuyi ta siya subar mai tsadar, already dama wanan sakon yakai ga sauran yan uwa ko, Wani irin shewa suka sa tare da yin ihun jin dadi a lokaci guda, Sai rawa da waka yabiyo baya tare da jin dadi, Mai,karatu kamar yadda ki, kasan cewa Joseph bazaiji dadi wanan zance,ba, dole baza,a rasa wasu masu irin ra,ayin shi daga cikinvsu, Kasancewar irin girman da churching ke da shi da al,iman da yatara a cikin sa, Kawai sai ganin wani dan matashi sukayi mai kamar shekara ashirin ya hau, munbarin maganar church din, Jin microphone na son magana kowa yai shiru aka juya don ganin kowaye, Michael wanda atare da iyayen shi yazo church din wanda ko hwanan hawar dayayi saman munbarin basu san ya hau ba,sai,ganin shi kawai sukayi asama,,, Nan Michael yafara magana kamar haka, wai may yasa mu Christian kullun maganar mu akan muslim ne, Maya sa su, basu damu damu ba, sai mu zamu dinga damuwa da lamarin su, Shin hakan na nuna cewa sun fi mu power in religion ne kokuwa, Su ma ai yakamata su dinga kawo muna wani hari amma sai banga sunayi ba, Wurin yagauraye da surutu, alokaci guda kowa na fadar ra,yin shi,, Joseph yaiwa su mama nuni da su tashi su tafi maman,Choima a lokacin tana wani daga hannu an yi masu wa,azin kwarai yau, Ejoma wace ke lura da yanayi Joseph itace ta riga kowa sauein mikewa tabi bayan Joseph din,,, Sun dawo gida cikin gajiya saboda dadewar da sukayi yau a church din, Mutane na taganin cewa yau an masu magana mai anfani sosai, ta yadda zasu samu galaba akan musulumai, Mamaki zullumi,da jimamay duk sun cika zuciyar Joseph, May yasa musulumai basu irin wanan sukar akan su, Don may ko yaushe basu da zance sai ta yadda za,a halaka musulumai, Alhalin su musulmai basu da wanan lokacin duk da su ma suna da laifi don suna yawan nuna kyamar su gare su, Hannu bibiyu yasa ya tallabo habar shi dasu ya kurawa TV da ke aiki ido tankar mai kallon abinsa akeyi a cikin TV,, Ejoma wace ke tsaye akan shi tana fadamai cewa akawo mai abincin sa a nan ne, Saida tai da karfi tace broda, yai yar firgigit yai wani ajiyan zuciya mai yar sauti, Ejoma takara gabatar mai da abinci a karo na biyu, Yace mata zaidai sha fruit kawai idan ya tashi yanzu yana son fitane, Ejoma tai yar fuska tace mashi please broda kadan ci ko kadan kafin kafita, Yai yar murmushi ta karfin hali yace ai bance banci ba kinsan cewa nayi breakfast kafin mu fita dazu, Ta dan zuburo baki tana nuna bacin ran ta saboda rashin cin abincin shi ko yau she,, Mikewa yayi yace su tafi yaje yaci yawuce tana biyansa abaya tana cewa sai kai broda na,. Yai murmushi don yana jin dafin kulawar da Ejoma ke gwadawa lafiyar shi akoda yaushe, A,daidai wanan lokacin wayar shi takara ana kiran shi, Ganin mai kiran shi yasa shi saurin daukar wayan kaunar shi Ruth ce ke kiran shi, Da sauri yadaga wayar yana mai fara zolayar ta amma sai yaji muryan ta tana kuka tana fada mai cewa mahaifin su ciwon shi yatashi na suga da hawan jini, Da sauri ya mike tsaye daga saman kujerar da yazauns don ya fara cin abinci, Mikewa yayu kamar wanda aka mintsina ya fada da karfi yace, yaushe May yasa ba,a fada mai ba sai yanzu, nan dai yai,ta fada akan rashi fada mai da ba,ayi ba sai yanzu yace mata zai shigo zuwa gobe, Daga haka ya mike baiko kara kallon gurin abincin ba, yana tafiya yana fadawa Ejoma, Haka kawai yaji wanan karon ciwon mahaifin nashi ya,taba mai zuciya, sosai fiye da koyaushe da a,ke bugo mai, Tunda safe yakama hanya zuciyar shi fam da fargaba tare da zullumi acikin ta don yadda yaji Ruth tana kuka a wayar Tafiya yakeyi amma hankalishi baya atare dashi sam ji yake tankar ya tashi sama da mota ahida Samuel ne acikin motar, Samuel wanda ke ganin irin gudun da yayan nashi keyi amma ya kasa magana a,ramshi dai yana addu,an Allah kai su lafiya, Sun kusa kawo wa kwantagora saboda irin gudun da yake shararawa a saman titin, Daidai wani kwana baiyi aune ba saiga wata motar irin ta kwasan shanui din nan, a wani kauye, ta debo shanaye zuwa wani kauye Aiko nan suka jamay motar su Joseph tashi kusan kasar motar,,,,, Bude idon shi kawai yayi yagan shi a gadon asibiti kwance, Andaura mai ruwa a hannun damar shi,, ga yan nurse nan na,ta yawo akan shi, A hankali ya dan kara lunshe idon shi ya mayar dasu ya rufe Yana kokarin son ya tuna ko a ina yake haka, don yakasa gane ko may ke faruwa dashi, alokacin, Zubur ya so, mikewa sai,dai ya ji andafe shi da karfi, Samuel, kawai ya iya furtawa a lokacin muryan Samuel din yaji yana cewa broda iam here,with u, Daga haka ya lumshe idon shi bai kara sanin inda yake ba kuma, Kusan duk wanda ke gurin zugun suke,cikin mawuyacin halin damuwa, Daga KB har jibrin duk sun halarci gurin duk tatare su da yan uwan Joseph din keyi alokacin, Anty Dije tare da yaran ta da Maryam dake tare da kawar ta SAFIYA, wace tazo yi wa Maryam din yini, Anty Dije tace su shirya sutafi diban Joseph din a asibiti, Ba yadda maryam ta iya ,dole suka shiriya, don bin Anty asibitin kamar yadda ta umurce su, Amma afili cewa tayi wa anty haba ai gaida mara lafiya lada gare shi duk dadai ba musulmi bane shi din, Sanan kuma aiko don Assalam dole ne in tafi in dibo shi Anty,,,, Malam A,A masuga sukaiwa magana, yazo kai su,, A, cikin shiga ta alfarma suke daga su har yaran don daka gansu kaga wayayyun yan birni, daga shigar su kawai zaka gane hakan, Leda tab da kayan fruit da kuma abinci a wani basket mai kyau, wanda aka dan lulube kulolin da ke ciki da wani kyale mai kyau, Shiko Mr Emanuel hankalinshi yai mugun tashi yadda yaga yaran gari hausawa suna tazuwa duban dan nashi mara lafiya, Bai,taba tsan manin cewa jama,ar da ake fadi yanadasu sun kai haka ba sai yanzu, Don haka tun da yaga Joseph din yadan samu lafiya yabukaci abashi, shi su koma gida adinga zuwa diba shi,,, Yayi hakane don ya rage yawan masu zuwa ganin shi kin san yadda yare suke da chanfi, Motar A,A masuga ta Parker a cikin haraban gidan Mr Ema din wanda yasha shuke ,shuken flowers masu kyau, Sai wani katon kare da suka gani daure da sarka, kaca, yana ganin su ya mike daga kwancen da yake yana wani gurnani, da haushi, Wa,iyazu,billahi inji Maryam, Cikin sauri maryam tayo baya inda anty take tana kokarin shige mata, A,A dake bayan su yai yar murmushi ya ce matsoraci, kada ki kada Anty pls, Amma jin maganae A,A din baisa ta rage shigewa jikin Antyn ba, Daidai kofar shiga falon gidan sukaga wani dan dattaijo zaune ya rike wata sanda mzi yar adon kamar kan mutum, Fuskan shi murtun kamar bai taba dariya ba arayuwar shi, Cikin ladabi suka gaishe shi har su Assalam yadda yaga su Anty sunyi haka shima yayi, Duk da shan tokan da Mr Ema yayi yana ganin ladabin su dole jikin shi yai la,asar, Duk da bai san ko suwaye ba, A,A ne ke fasa mai cewa sun zo gaida Joseph ne, Da hannu ya nuna masu kofar wani falo cikin hausar shi tayare mai nuna kasaita, Yace ku shiga yena ciki, Wani makeken falo ne agaban su A,A dake gaba yai yar sallama irin ta kafirai, Suma sukayi kamar yadda sukaji yayi, suna bin sa a baya, baya, Wata yar tsohuwa suka gani zaune a falon saman wani tafkekiyar kujera ta alfarma,mai kyau da laushi,, tare da wasu yan mata biyu sai wani dan karamin yaro da sukaji sunan shi wai Jacob, Yan matan suka amsa masu tare tare da nuna masu kujera su zauna, Nan suka gaida su cikin mutunci kamar yadda suma suka tare da mutunci, Maryam sai kallo takeyi tana dan yatsine fuska duk da gidan yai madu bazata Don kamar ba,acikin kwantagora suke ba, lokacin, Malam A,A yace madu munzo gaida Joseph ne ko yana ciki, Yar tsuhuwar nan taiwa yan matan wani yare, na IBO tana mai yamutse fuskan ta, Sai gudan mai wani dan guntun buje iya cinya tace yana barci pls, Maryam kallo guda tai masu takauda kanta gefe guda don takaici, Ejoma ce tace wa Ruth da yaren su haba kibari su shiga mana tunda har kikaga baba yabar su sun shigo, Ku shiga ciki ta nuna masu hanyar wani dan siririn corridor, tace yana ciki, Nan suka mike suka shiga inda aka nuna masu, yana gurin, A lokacin KB da Jibrin duk suna gurin shi atare da shi, Wani da ga cikin yan uwan Joseph mai hausa badarniya yace kutafi pls yana barci ne, Maryam ta bata fuska tare da hararan mutumin Ejoma wace ashe tana bayan su tace kabari su shiga baba yabarsu suka shigo Dan takawa sukayi suka isa inda yake kwance saman wani tafkeken gadon mai cin kusan mutun shidda, Idon shi a rufe kamar mai barci saidai ba barcin yakeyi ba, Yana jin duk abin da akeyi, Kafar shi da hannun shi suna daure da wani bandeji fari kal, Duk wa yanda ke gurin sunyi zugun ga wani a tsaye da alamar likitane,shi, Assalam naganin shi yace little mummy kamar Uncle Joe, A hankali ya bude idon shi don jin muryan Assalam da yayi, Kallon su yakeyi gaba dayan su da suka shigo dakin, alokacin, Dan murmushi ya kago a fuskanshi duk da zafin ciwon da yake ji, A hankali suke gaishe shi fuskan su fal da nuna tausayin sa, Shima dai da kyat yake karba masu, gaisuwar cikin nuna kulawar shi , Yanabinsu daya bayan daya da kallo har idon shi ya sauka,akan maryam Irin kallon da yai mata yasa A,A dan juyawa don yaga ko itace yakewa wanan kallon, Saidai yaga Assalam rugumay a jikin Maryam din , Wanda alama yanuna yaron yake kallo, ZEEEE MAKAWA [2/21, 9:11 AM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA A cikin cijewa da daurewa ya furta sunan Assalam a hankali, Yana mai kokarin yi mai alamar da ya karaso gurin shi, Malam A,A shida KB suka gane mai yake nufi da yaron, Suka ce Allah wai kazo inji uncle, cikin sauri Assalam yadan make hannun shi alamar bai zuwa, ya shige cikin jikin Maryam wace ke rike dashi tun shigowar su, Dariya kowa yasawa Assalam din wanda ke gani kamar ba Joseph din daya sani, bane a kwance, Don ganin irin bandejin da akasa mai fari kal a hannu da kafa, Ànty Dije tace Assalam baka zuwa gurin uncle yau, Joseph dake kokarin nuna daurewar shi, da kuma cije bakin shi don ciwon da yake ji, Ganin irin wanan yanayin da yake ciki ne yasa maryam duk taji tausayin sa ya kamata a,ran,ta, Bata san lokacin da furta a hankali ba murya kasa,kasa, da Sannu ya jikin, Da, sauri Anty Dije har A, A, suka waiga ta don jin furucin ta yau akan Joseph wanda arayuwar ta taki jinin shi saboda baya sallah, A hankali cikin cije bakin sa yadan furta, a hankalo cikin dauri, Thank, 'God, "Nagode, Yace cikin murya maiban tausayi, irin ta marasa lafiya Sai a lokacin jin dakin yayi tsit alokacin maryam ta dan tsargu, da cewa kila ita ake kallo, Da wutsiyar ido tadan kalli, gefen ta aiko ita dince malam A,A kewa kallon mamaki shida anty, Kata na a dan sunkuye a kasa ta ce a hankali safiya mudan fita daga waje har su fito, Tayi hakane don tafitar da wani abu azukatan su,a lokacin, Yin hakan ko yadan wanke ta ga A,A wanda zuciyar shi tadan rude duk da yasan cewa ba wanan ga Maryam Don ita yarince mai kishin addainin ta sosai,ba,ata taba hurda arne ba arayuwanta ko ta arziki ne, Daidai zasu fitane saiga Aisha da Amina cikin shiga irin ta wayayyun yan mata Dauke da wasu irn manyan ledoji a hannayen su,sai tako sukeyi guda, guda, Wani irin mugun kamshi duk ta gauraye gidan da maryam ke ta tsandar zama, tun shigowar su, Joseph yadan so yamike amma san yakasa cikin dauriya yace wa su maryam da safiya, nagode sai anjiman ku, Aisha tabi su da kallon mamaki don sam bata gane cewa maryam bace Ita a,zaton ta wasu yan matan shine can sukazo gaishe shi, Har ta fara masu kallon kunyi kuskure yan mata, Sai idon ta ya sauka akan Anty Dije wace ke zaune saman wani kujera dake facing din inda Joseph yake tana dauke da Issalam, Dan dariyar yake tayi don ganin tare da Anty wa yan nan zukazukan yan mata suke, Nan suka gaisa sama sama da,su suna mai kara tambayar ya jikin shi, Aisha don nuna kosawa da kuma waye wa sai zare dan gyalen da tayafo saman jikin ta tayi Tana kokarin zubawa Joseph abincin da suka shigo dashi, Shikuma daga kwance yai nuni da a,a yana kokarin nuna wanda su Anty Dije sukawo, Wani iri Aisha taji a lokacin, azuciyar ta tace ya kamata fa tai maganin wanan matar haka wace Joseph ke kulawa tankar yar uwar shi, Amma afili sai tai wani murmushi, Mr Ema yashigo yana fada cewa bai yarda kowa yakara kawo ma dan shi wani abu ba, Yanata fada da su Ejoma da Samuel har maman Choima, Joseph cikin karfin hali ya dan nuna Anty yace she, is my sister I always eat from her when I was in the town, Da mamaki Mr Ema ya waiga gurin Anty Dije don ganin matar da Joseph yace itace mai bashi abinci, Kara cika mai ido tayi don sai yaji bai iya cimata mutunci akan yadda yake rufe idon shi yai wa wasu, Kamar zai yi magana sai kuma ya sa kai kawai yafita, yabar dakin, Sai a lokacin Assalam yadan rarafa zuwa gurin Joseph ya zauna gap da shi, Su maryam suna falo zaune ana kallon kallo tsakanin su da mama da Ruth, Ejoma ce tafi tadanzo inda suke zaune cikin matsuwar su Anty su fito subar wanan gidan maikama da kurkuku, Jin takon su fitowa yasa saurin mikewa don shirin tafiya, Ànty tace bazaku shiga kuyi sallama dashi ba, Kai maryam ta kada mata alamar aa, Sun danbar gidan maryam tai yar siririyar ajiyar zuciya mai nuna wani alama, Sai a lokacin A,A yace gaskiya ya na jin jikin sa sosai karfin haline kawai, Anty tace ai ga yadda ake fafi ba,a sa rai cewa sun fita daga cikin motar, Maryam da sai yanzu tai magana tace da yamutu a kafiri kenan, Kai, kai inji anty Dije wacce sam bata son wanan halin na maryam akan wanan mutumin watau, Joseph, Dalilin wanan accident din na Joseph aka dage bukin KB Wanda shi KB din da kan shi ya bidi alfatman cewa yana son adan daga bukin don wasu bukatu nashi, Shiko yana ganin cewa hakan baidace ba ace yana bukin shi ga Joseph a kwance ba lafiya wanan ne dalilin daga bukin da yayi, Sannu, sannu akwana atashi Allah yaba Joseph sauki, Tun yana dan iya fita kofar gidan su har yadan fara bin abokai suna kaishi yawo cikin gari, Yau ma kamar kullun dayake damana ya sauka akasa ruwan sama yafara samuwa, Hadari aka hada sosai ko ina a gari yayi jajir da alamar akwai iska atafe da wanan hadarin A lokacin Joseph yana tare da yaya illiya hira wanan hadarin yataso, Sanin cewa bawai, kafar mai lafiya gare shi ba sosai a lokacin Hakan yasa shi barin har iskan yadan rage ko agama ruwa, Iska sosai akayi sai dan yayafin da ya biyo bayan hadarin wanda ba wani ruwa mai yawa akayi ba Suna fita waje sukaga yadda iska yaiwa mutane barna sosai agari, Yaya illiya na cewa subbahanallah shi kuma Joseph cikin kidimay wa yace, Allahu Akbar, Da sauri yaya ya kallo shi da wani irin mamaki, don ji yayi kamar ba shi bane yace hakana, Sai kuma Jesus crisi muna ciki haka akai wanan iska haka, Bayan sunyi sallama da yaya illiya, ya kama hanya zuwa gida, A hankali yake tafiya zuwa gida, a lokacin saboda yana dan lalaba kafar shi ne, Kusan zuwa unguwar su yaga gidan wani malami da ake cewa,,MUSA, JA, don mutumin fari ne sol, da shi, Yasan shi tun yana yaro yakuma san gidan shi a cikin uguwar tasu, Gidan yaga ni duk katagar gidan azube duk mai wucewa yana ganin shi, Malam musa ja Joseph yagani yayi tagu a saman dakalin kofar gidan shi, Ga matan shi duk mai wuce wa yana gani sai kuma wani makwabcin malam musa ja, Shima gidan shi tsohon gina ne sosai don duk haka su ka taso suka ga ginan har yanzu suna dan maneji da abin su, Har yai kamar ya wuce sai kawai yaji bazai iya ba don haka ya yo ribas baya da motar shi, Cikin dan dangyasawa ya isa ida mutanen suke tsaye cirko cirko Ya ce malam yau kuma abinda yafaru ke nan Allah ya sauwaka, Sukayi mai godiya kula masu da yayi ya juya yana mai jumamay abin Abin na malam musa da makwabcin shi yafi yawa, Don su ga zubewar gatanga ga kwanon ginan ya hankade ya kware sama, Sun dade da mahaifin shi a waje suna maganar wanan irin iskan da tazo wa mutane yau, Nan Joseph ya ba mahaifin shi labarin makwabtan su, abinda iskan yai masu, Yayi tsan manin zai ji yace masu koda sorry ne sai kawai yaga ya yi murmushi, Shiko Joseph duk tausayi su malam musa ja ya kamashi da wanan tunanen ya kwanta, Saidai sam barci yaki daukar shi saigani irin halin da yaga su malam musa da makwabcin shi aciki yakeyi, Wayar shi ya lalubo, nobar Hamza yakira,don su KB da,Jibrin ba su gari, Nan yai mai irin bayanin abin da yake so yai mai tunda safe saboda yanzu dare yayi ko, Waahe gari hamza ne tare da wasu magina sukayi wa Musa,ja, sallama Hamza yai masu bayanin cewa wani bawan Allah ne ya ruro shi a gyara masu gida amma yace kada a fadi sunan shi, Gyara sosai akayi don dakuna hudu akaja wa musa ja, shima makwabcin shi am mai daidai irin da ya rushe, Aikin cikin yan kwanaki aka gama komai kamar yadda yaso, Kafin agama aikin Joseph yasamu kira na gagawa yabar gari, zuwa diban depot din su da gwaunati ta bude Ya koma da kwana biyu saiga su malam musa,ja sun samu labarin cewa, ashe Joseph ne ya taimaka masu daga wurin wani ma,aikatan ginan da sukai masu, Aiko Mr Emanuel maimakon yai murna saiko ya hau masifa dasu ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, Harda cewa wai hausawa sun yi wa dan shi charming, In ba hakaba ba ai yu,yu yadinga madu wanan dawainiyar ba haka, Anan mutanen gari suka san cewa Mr Ema baison irin taimakon da Joseph kewa mutane daga cikin dukiyar shi, Kowa ya shiga fadin albarkacin bakin shi, akan Joseph, din, Joseph yasha fada mai tsanani sosai gurin mahaifin shi akan irin taimakon da yakewa hausawa Karshe yai warning din shi kwarai da gaske akan in har yakarajin haka zai dauki mai mataki mai tsanani, Bayan sun gama wqyan Joseph din yai yar ajiyar zuciya yana madaga wayan nashi yabishi da kallo Kamar wayan ce taimai magana hakanan har ta bata mai rai, Yàu ta kasance ranan litani,itace ranan da ko bature na tsoran ta, Cikin sauri Maryam ke komai don gudun makara, Sai,dai duk saurinta, yau din ta dan makara, Tun,da ga bakin gate ta hango malam A,A shima kusan a lokacin, yake shigowa, school din, Daurewa tayi kamar bata gan shi saboda yawan jama,a dake gurin, Yana gama parking yai kokatin kiranta da waya sam maryam bataso haka ba, Saboda bata son mutane sugane cewa akwai alakar, soyayya a tsakinin su dashi, Daidai lokacin da yakaro inda take tsaue tana jiran isowar shi, Da murmushi fam a fuskan shi ya karaso gurin ta, Yadan dubi agogon hannun shi yace yau dai babu saurin shigewa ajivda guri don gadhi kusan tare muka iso yau din, Maryam tai yar murmushi tana, dan kauda kanta gefe cikin kunyan shi da takeyi kamar kullun, Ta ce aiko yau saboda nadan bata lokacine har na makara da bazaka gan ni ba sai tashi, Yai yar mushin jin muryan ta cikin dadi, yace, tau yaudai karfe nawa zaki fito, Tace mai sai biyar, Yai murmushi yace to saboda zan zo in dauke ki muje gaida hajiya ta da tazo, Gaban maryam ne yafadi don jin abin da malam din yace, Duban shi tayi da mamaki tace a hankali haba malam kaga haka zai yi ace ban ko fada a,gida ba zan tafi gaida mama, Maryam ke nan may ye aciki don kn tafi daga nan ko haka Ina iyaka dai ku,gaisa da ira, kawai ko, Gaskiya bazan je ba sai na fadawa Anty tukun duk abin da tace shike na, Daga haka tajuya tai cikin makaranta abinta, shiko binta yayi da kalo cike da mamaki irin halin maryam, Har suka tashi daga school bata kara jin motsin A,A ba Abinda yasa ke nan tagane cewa yayi fushi ne da ita rashin yarda da maganar shi don zuwa gai,da mahaifiyar shi da tazo daga Abuja,, Koda ta dawo bata boyewa Anty komai ba ta fada mata yadda sukayi da ,A,A din Anty tace kin kyauta Maryam shi yasa har kullun nake alfahari da ke wallahi, na kasan cewa yarinya mai la,dabi da biyayya dakuma sanin ya kamata Amma tunda har ya roka sai yazo ta nan gida yadauke ki ku tafi yafi mutunci,, Don yafi ace kin bishi daga can sam babu mutunci a hakan , Kiranshi tayi cikin lalashi tai,maganar kamar haka, Malam munyuni lafiya, sai kawai naji shiru ina ta jiranka tun da zu, Uhummm kawai yace kin gama jamin aji ko maryam, Don kinga banda yadda zanyi da kaina ko amma babu komai Anty ta yarda ki tafi ko tadan marairaice muryanta tace eh ta yarda, Ok yace sai ki shirya kafin inzo, don muje mudawo da guri, Zani da riga tadaura sai hijab da tasa wanda yai dan shige da kayan jikin ta, Turaren ta shafe jikinta dashi na black oud, na mata, takalmin ta flat shoes tadan sa, Ba bata lokaci A,A din ya iso saidai ya ganta da Issalam yai yar murmushi don yasan hakan wani hikima ne na manya, Gidan gaskiya yakai gida don dagani kasan cewa, akwai wadata a gidan, Wani katon falo ne suka dosa, maryam tana rike da hannun Issalam, A,A ne gaba suna bin,shi baya da sallamar shi ya shiga gidan, Wasu matane zaune su biyu saman wasu laulausar kujeru ga carpet amalala akasan irin ta masarautar nan, Hira matan biyu keyi, alokacin amma una sallama sai an,nurin dayar wace itace fara, yadushe, Nan da n ta bata rai kamar batai farin ciki da ganin su ba, Maryam gabanta yafadi duk bawai sanin ta tqyi ba Amma bataga farin ciki ba ga fuskokin su, Kasa maryam ta zube tana mai gaishe su cikin ladabi, Kanta na kasa tana rike da hannun Issalam tankar za,a kwace mata ita, Shima dai gaishesu yayi a cikin ladabi, ,yakuma ji dadin yadda maryam din tai wa mahaiyar tashi, Dayar matan mai fari da kiban jiki, wace da ka ganta kasan yar Royal family ce, Tace ka kaita gurin su ,Assy, su gaisai sai kadawo, Dakin ya nuna mata saboda shi baya shiga,dakin kan,nennashi Saidai maryam dn nadhiga sai taga dakin babu kowa don haka sai tayo baya daniyar komawa falon , Muryam matar taji cikin fada tana cewa May kake nufi da kawo min wqnan bakauyar yarinyar Dan mama, Cikin murya mai taushi yace ita nake son in aura mama, Abinda maryam taji yakusa sata sakin fitsari alokacin Amma sai ta daure ta fara,addua daga bakinta,har cikin ranta, Kafita idona wallahi na fada maka nariga nama mata ba yau ba Da akwai abinda nake jira shiyasa ban ta da zancen ba shi ne don baka da kunyazakaje kadauko min wanan yariyar wai matar da zaka aura, To tun wuri ka ba kanka shawara tun ba,a jimu ba,in ba hakaba zan bata maka rai sosai wanan karon, Daga haka maryam tafito daga inda take tsaye tun farin maganar su, Firgit ya waiga don yaga ko taji zancen mahaifitar tashi, Amma sai yaga fuskan ta da yar fara,atana cewa zan koma mama sai anjimar ku nagode cikin halinta na alkun ya, Hararan ta uwar tayi da wani irin yanayi na bayabo ba fallasa, Sai dayar matace ma tace to ku gaida gida mun gode ko, Ko a mota sam maryam bata nunawa A,A cewa taji zancen shi da mahaifiyar shi bba Ba karamin kokari maryam tayi ba wuri control din mind din ta,don ko anty takasa fadawa wanan zancen,ba, aranta tabarshi, Dasauri tagama abinda takeyi aranan tashiga daniyar ta kwanta ko zata danji sanyi aran,ta, Sai taji yanzu maganar ta dawo mata sabo, Batasan lokacin da hawaye masu zafi suka fara gan garo mata ba, Jin hannu tayi an dafa mata kafadar ta, ko bata waigaba tasan ce wa Anty Dije ce, Wani sabon kuka tasake cikin tashin hankali, ita ma antyn kukan takeyi, Saida sukayi mai isar su suka bari don kan su, Nan maryam ta kwashe abin da taji mahafiyar ,A,A nafadi tafada mata, Shawaran da Anty Dije tabata shi ne tabari suga matakin da A,A, din zai dauka,,,,,,, ZEEE MAKAWA [2/21, 9:13 AM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣6⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,, Assalamu Alaikum yan uwa musulmai kutayani yiwa Anty na Anty NAFISA ALIYU HARZAMI,,Addu,an, samun sauki,,cikin dan lokaci, Rayuwa yau da kullun batabar komai a sannu a hankali maryam ta fara walwale wa, daga damuwar da tashiga, Saidai shawaran anty yai mata amfani, sosai don har yau A,A Masuga, bai nuna mata komai, Sai kara nuna mata kulawa da ya,shiga yi fiye da, farko,,,,, Wanan dalilin yasa ta manta zancen mahaifiyar shi a rayuwar ta , Don dai tasan cewa bada ita zata zauna ba da shi ne, Shikuma bai nuna mata gazawan shi ba akanta kullun kara son ta yake ji saboda irin kyawawan halaiyar Akwana atashi hasarar mai rai, saiga lokacin bukin KB yazo, Don haka suka fara zama busy da aiyukan buki duk a gidan su KB din ake sha,anin to amma angwanai suna,zamane a falon yaya illiya dake fuskantar baban titin cikin garin, Wanan bukin yadan sa maryam dan sakin jikin ta da su KB Don duk wani abin bukata, dasuke so maryam ce zasu kira saboda abokan su da suka,zo daga nisa, Matar malam suke cewa maryam inda itako abin na mata dadi arai,sosai, Ilimi, arziki, kyau, wayewa, wani abune, wanda baiwa ce daga Allah, Shike ba duk wanda yaso ako wani lokaci, ko yanayi, Wai duk taron nan na buki KB da matasa masu jin kan zu keyi, Zuwan Joseph a cikin su duk sai ya dakushe sauran, kamar ba,ayi da farko, Yana isowa buki ya canza sallo, nan take komai aka fara yin shi acikin morewa rayuwa, dakuma wada ta, Baki sun zo daga nesa saboda wanan bukin na KB wasu daga ban garen sanar shi ta Gas Wasu kuma abokaine da aka hadu ta wani sha,ani, aka zama daya, Maryam ta kira safiya don ta taimaka masu da aiki, tare da,wasu makwabtan su yan mata, biyu, sai kan,nen mijin Anty Dije su uku, Shanu Joseph yasa,aka yan ka anan bangaren ango, da suke , Yasa Anty Dije tayo hanyan yan kwatakwali togo, masu aikin girkin abinci, Nan da,dan guri ya kici may da taron hayaniya, ga raguna uku da yasa a gyaro akawo duk wurin anty inda yace anan za ai masu nadu girke,girken, Saboda bazai kai gidan su ba don mutane wasu baza su ci ba idan ance acan akayi, Duk wanan aiyukan da mutanen da akadauko sukeyi bai hana maryam da kawayen ta zakewa ayi shi da su ba hurjanjan suke aikin su tsakani da Allah, Abincin da akafitawa baki da shi a wani guests house, bai ko isa ba saboda irin haduwar da abincin yayi, Hakan yaba Joseph da jibrin dadinkar kayan hada hadadaen abinci, don kara yawan shi, Suna tsaye a filin tsakar gidan Anty shi da jibrin cikin shigar kananin kaya masu tsada, Dagani basai an fadama irin haduwar su,ba, Jibrin yace gaskiya anty kin muna abinda ma bamu zata ba zokiji yadda bakin mu ke santin abubuwan da aka kawo masu, Anty Dije ta nuna masu maryam da su safiya tace kun ga wa, yanda sukai maku can, don ni har fada naso yi da su da farko, Kallon inda su Maryam suke sukayi gaba dayan su, alokacin suna kokarin yi masu tuwon dare, Jibrin ne ya tako har gurin su,yakaraso yana ce masu sannu ku fa, yan mata, da kokari, Suka amsa mai kowace tana kokarin nuna kanta gareshi, In ka dauke maryam da kawarta dasuke can ta cikin kicin suna hada perpepsoup, din kayan cikin rago, Ga mamakin maryam sai kawai ganin jibrin din tayi har cikin kitchen inda suke ya biyo su, Yana ma safiya wace ke kokarin hada jajage a tukunya, Wani irin kallo wanda ke da ma,ana ga wanda akeyiwa, Haba Maryam baki bari ta huta hakanan sai ki dinga bata wahala, Maryam da mamaki take kallon jibrin din yau wanda zata iya cewa bai ma san sunan taba sam, Don basu maganar komi a tsakanin su sai gaisuwa, Saigashi yau yakira sunan ta harda ba,a yake mata, akan wata, Maryam da ta gane nufin shi sai ta ce mai ya jibrin ko ka manta a kitchen kake yau, Yadan waiga cikin nuna ko oho yace an, hana maza shiga kitchen ne, Dariyan da maryam ta kumshe saida ta fasa,shi a fili, So sai take kyalkyallan dariya har dan diplo din ta na lutsawa fararen hakoranta da ke boye ko yaushe yau su,ka haska, a fili, Ba jibrin dake kusa ba har Anty da Joseph dake ta waje saida hankalin su yakai garesu, Suna mamakin may jibrin ya cewa maryam haka yau take wanan dariyar, Basuyi aune ba saiganin jibrin sukayi ya karbi cibin miyar hannun Safiya yana motsa miyar duk gidan kallo yadawo gare shi, Ba fatima ba harda Joseph saida ya murmusa yau, Da sauri yafito yana yarfar da hannun shi wai zafi dan ruwa zafi ya dan tsirgo mai a hannun shi, Dariya aka karasa mai ba shiri ya jawo handcarchef din shi yana goge hannu da zufa, Hmmm kawai,, Joseph yace daga karshe don ganin irin tabar da jibrin ke yi, Har ya kai gap da fita waje ya waigo cikin irin tafiyar nan tashi yace, , Meet, me outside pls, Jibrin har ya fara tafiya sai kuma yadan waigo ya kalli inda maryam take tsaye yace, Kauna ta zan gan ki in ,nadawo, pls, Aiki sosai suka sha ranan nan, ana gobe daurin aure suka shirya wani irin gagarumin friend's day, wanda abokai da yan,uwa za,su,halarci wanan bukin, Maryam dai dama bawai ta na zuwa irin wanan bidi,ar bane don haka sam bata sa rai cewa zata,ba, Amma sai ga anty tashigo da,wasu din kunan wasu indian materials masu kyau da daukan ido guda biyu, Ita da safiya saidai kowace da kalar nata, dinki daine iri daya, sak, Sunji dadin wanan kayan sosai sai dai da anty ta,bukaci zuwa gurin bukin duk suka,bata fuska Jibrin ne shigo dai dai lokacin, yace yauwa Maryam wallahi ina ta sauri don inzo in samay ki, Don ban da nobar wayan ki da na kiraki tun can in fada ma,ki, Gefe dan je da ita, inda ba mai jin su, yace yauwa, Maryam dan Allah magana zan yi da ke a kan kawar ki, Maryam tace wata ciki, yace haba kindai gane mana, wanan da kuke tare koda yaushe, Wallahi tun ranan da na fara ganin ta naji ina mutuwar son ta, sosai, Don Allah maryam ki taimaka min kada son ta, kawar ki ya kashe maki yaya maryam, Maryam tace, a,a a, gaskiya ba ruwa na kasan halin yan matan ku kada,su samin kawa a gaba, Ke maryam ban don sheri ni kin taba, gani na da wata, wai budurwa, Kai ya jibrin wa,yan nan yan gayun yan matan naku da suke biyo ku har gida, Wa,wai su Aisha ai ni wa yan,nan ko kallin arziki badu isheni, ba balle, Wallah kasan koni kaina har gobe zargina sukeyi don wani kallo, naga suna min, Kai maryam, idan sukai mata wanan kallon wallahi, sai naci uban su su dukka, Da mamaki jin yadada ya ke kalamsi akan safiyar ta, To ya jibrin Safiya fa ba, irin yan matan ku ba ne don ba wata yar gaye bace, Kaga bazaku dace ba, don kun fi karfin ta gaskiya kabari tasamu,dai,dai ita, Kai maryam don Allah kada wanan yadamay ki, ai ninr zan haskata sannu a hankali ko, Wallahi auren ta nake son yi kuma bawai ina son abin yai wani dadewa bane, Amma yanzu ki, fara hada mu, insamu in kafa kaina agurin ta, Sanan , don Allah, ko anty kada kibari taji mubar abina tsakanin mu, har ya zama gaskiya, Shiru maryam tayi tana dan nazarin maganar, shi ,ko gaskiya yake fafi ko kuma yaudara ne, Can tace shike nan ya jibrin, tunda kace haka yanzu yakake son ayi? Yauwa maryam kinga, indan zamu tafi gurin friends day, Sai kiyi kokari ki hadamu a mota guda dag nan zan fara kafa kaina gareta, Bayan rabuwan su sai maryam taji abin yai mata dadi, saidai tana zullumi kada yazo ya yaudare ta daga baya don su gogagun ne sai manyan yan mata, Maryam wai may kike yi ne tundazu baki gyara guri,ba balle ki shirya ba,ga,kina da alamar zuwa ba fa, Anty ina magana ne da yaya jibrin dama yanzu nake son in hada Ta waiga inda Safiya take tana dan gyaran dakin da suka bata, da tarkace dazu da suka taru, Tace ma safiya barin dawo musa labule dake safiya, akwai alheri tafe insha Allah, Safiya ta kama kallon ta, kawai don bata san ko may maryam din zata fada mata ba, Saida suka gama duk abinda sukeyi acan cikin dakin maryam suna shirin tafiya don har anty ta shirya yara ko, Safiya ce ta kasa hakkuri ta ce maryam wai may ye kika ce zaki fada min dazu, Hannunta maryam tadan riko kadan, ta dan kura mata ido na wani dan lokaci, Sai kuma tai shiru, tace wallahi har na rasa ko ta ina zan fara zancen, Ikon Allah inji safiya, wace itama maryam din take kallo, Fada min don Allah kin sani, cikin duhu wallahi, Maryam tadan nisa sai kuma tace wallahi safiya,duk ma na shiga rudani wallahi, Dama wanan ya jibrin din ne yace in fada maki wai yana son ki kuma waida aure,, Kai haba maryam don Allah ki daina wanan zance ina,ni ina wayan nan mutane Aina fada mai haka safiya amma sai yace min shi wallahi da aure yake son ki, Hmm maryam amma kin san cewa mu gidan mu talkawane lis,don bamu da komai, Don haka ba,an sa kaina cikin wahala ba wallahi, Inda dai talaka ne iri na ba zan ce maki no ba , Kai safiya wayasan gobe ban da Allah, balle har ki saurin yankewa kanki hukunci haka, Ni shawaran da zan baki yanzu shine tun da har shi ya nuna yana sonki to Sai ki gwada sa,arki mugani ko Allah zai sa shine mijin naki, Iyaka dai ki kara kama kan ki sosai dashi kin san su sun saba da rayuwar, wayewa, Maganganun maryam sun sa safiya tadan yi sanyi ,don gaskiya tafada mata, San ai aure yin Allah ne bawai zabin mutum bane, sai in Allah dama ya nufa, Maryam ta mike adaidai lokacin da tajawo kayan da zasu sa agaban tace, Kada ki cuci kanki safiya don nima kinga lokacin haka, nayi amma sai nazo na fadawa Anty, Don alokacin ina ganin cewa ga yan mata nan wayayyu a cikin FCE amma zai buge da cewa, yana sona sai kawai nadauka yaudarata zaiyi kawai, Ashe abin ba haka bane,,hadine daga Allah, Marya tamike tsaye tana kokarin walwale kayan don su diba dinkin tace, Tace don Allah safiya ki daure yau ku dan gana dashi, don muji ta bakin shi Kinfa yace min ma wai shi zai tafi dake gurin hall din ajima, Kinga ko inda bada gaske yakeyi ba da aibazai yi kokarin nuwa duniya ke ba, Dan siririn ajiyar zuciya, safiya ta sake tace maryam bawai ban son hakan ya kasance bane, Ina dai gudun abinda zai jawo min fitina ne kin san halin da mahaifiyata take ciki kada in dauko mata magana, Amma ba komai tunda naga kin yarda dashi don nasan cewa bazaki kaini mugun wuri ba, Wayar maryam ne yai kara,a,lokacini ko bata dauka ba tasan cewa A,A din tane akan layin, Cikin kashe murya ta dauki wayan nan yake sheda mata cewa tajirashi zai zo ya kai su gurin bukin, Duk da dai bata gaiyyace shi ba tun farko, Maryam tadan kara kwantar da muryan ta tace malam nasan cewa baka wani hurda da sune shi yasa ban fada ma ba, Yai yar dariya, yace wallahi jibrin ne ya fadamin dazu da muka hadu gidan mai dashi, So ki bani nan da minti ashirin zan iso, insha Allah, Kayan da su maryam suka sa yai bala,in fitar dasu sosai, Saboda bawai samun irin materials din akeyi ba akon,ina don haka sai yazama wani abin kallo, ga jama,a, Tsab suka fito gaba dayan su a lokacin, Safiya sai faman koda shigar maryam takeyi ita ma maryam din hakane, Jibrin yazo har ciki da kan shi yana fadawa maryam cewa tafadawa safiya yana waje yana jiran ta, A,Daidai lokacin A,A ya iso don tafiya dasu kamar yadda yace zaizo yakai su, A,lokacin wani kanin mijin anty Dije ya zo don yakai su Sai ya tar da za a kaisu amma Anty dije sai tace ya tsaya ya kai ta ita, A hankali suka fito saida ga motoci nan gurin zakace ko a gidan ne ake bukin, Har bakin motar jibrin Maryam ta raka sadiya tadawo, Ta bude motar A,A, tashiga A,A din yadan waiga yakalli inda maryam take yace, Ina ita safiya din, kuma,? Tana can a motar jibrin tare zasu, Tafada a takaice, Wani irin kallo A,A din yai ma ma maryam. Yace kina da hankali kuwa, yarinya tazo maki buki sai ki bari tabi wani kato, Maganar yaba Maryam mamaki, tace jibrin fa nace ma malam, Yai yar tsuki Mtsss, maryam ban zaci har zaki amince da safiya ta bi wa yan nan da kowa yasan yan duniyar yarane, ne ba, Yaran da duk gari ankasa gane sanar su har zuwa yanzu Tunda yafara magana maryam kallon shi kawai, takeyi Tace haba malam nafada ma cewa ba abin,in da zai samu safiyan, Ya dan daga mata hannu yanu nna mata alamar ya isa hakanan, Har suka kai gurin bai kara mata magana ba, Gurin yacika fam da jama,a lokacin har, kujeru sundan kare daga ciki, Wasu ne sukazo suka yiwa su maryam kwantace da wasu kujeru a can gaba, A kusa dasu taga harda su anty dije suna nan gab dasu, Basu wani dade ba akafara program din inda aka r da Amarya da ango, Kujerun wasu yan mata dake dan nesa dasu kadan, Taga ana dan nuno su a hankali bada wani jimawa ba taga A,A ya mike zuwa wajen yan matan,,,, ZEEEE. MAKAWA,,, [2/21, 9:15 AM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Jinjina gare tare da fatan alheri ko yaushe Anty Nafisat, Aliyu Harzami, UmmuFadleeh safeenat Abuja, Mamam farida,Maman Walid, Maijidda Harzami, Mariya SB, Jamila Sifiyanu,Anty na hafsat Yusuf, da members din Zeee makawa novel, da members na takari novel Ina maku fatan alheri dacewa da Rahaman ubangijin mu, da kuma gamawa da duniya lafiya, JUMM,AT, MUBBARAK👏👏👏👏👏👏👏👏 Zaune take daga inda A,A yabar ta ko zataga dawo wan shi sai kawai taga tun yana yar kus,kus,da wanan matar da taga yaje gurin ta har sun kwasa sun fita, Shigowan Joseph tare da,Aisha yasa ta dan daina kallon hanyar dataga A,A din ya bi, yafita, Joseph da Aisha tare da Amina sun shigo cikin wani irin shiga ta alfarma, Don dai ko makiyin su dole ya yaba ma shifagar su, Aisha ba kunya tana make da Joseph gam saboda ta bushe fitilar ta bata kunya kowa agari, Yan wasan gidan mai Jauje na kwantagora sun fito sun yi wasa, Sai wani mawaki makwabcin garin kwantara daga KB state garin Yauri Sani Aiyu dan Dawo shima yafito yai nashi wasan Nan masoyan Joseph da bakin su suka dinga barin kudi ga mawaka, Daga karshe aka dan yi traditional show na yaren da ke cikin kwantagora, Toran kawa, kambari, Dukkawa, Dakarkari, pure hausawa, da sauran su, Wayan Maryam wace takai iya wuya, yai yar tsuwa, alamar sako ya shigo mata, Budewa tayi sako tagani kamar hàka Ki, yi hakkuri pls Maryam, bazan samu mayar, da ke, gida ba , Ku komatare da Anty pls, Abinda aka rubuta ke nan a sakon , atake maryam ta fahinci, sakon daga, A,A masugane, Wani iri maryam taji a ran ta, maganar da ya fado mata arai shine, muryan mahaifiyar A,A alokacin da suka je gaida ita, Daga haka tamike tsaye daga inda take zaune, Tafiya takama yi cikin tashin hankali take dan takawa, Sai muryan Safiya taji a gaban ta tana cewa, banga motar A,A ba a waje maryam, Dan ajiyar zuciya tayi don ta riga tayi nisa gurin tunane , Tafe suke a motar jibrin sai hiran wasan nin da akayi akeyi amma ita sam hankalin ta bai tare da ita, Abinda zuciyar ta ke tambayar ta shine wacece wanan da A A yaje gurin ta, Har tasa shi fita hall din taron yakuma iya wucewa ya bar maryam din, a gurin,,, Har suka isa gida ,hankali maryam atashe yake gashi suna da aiki so sai don gobe daurin aure su zasuyi abincin reception, Jiki ba kwari ba ku,zari haka ta, daure, tayi aikin cikin bacin rai tun bata walwala har ta dan sake jikin ta don taga amfara tambayar ta komay ya,samay ta, Shiko A,A tun fitar su waje da kaunar maman, da suka hadu agurin bukin, Sun kwashi lokaci da ina yana kokarin fahintar da ita akan maryam din, Amma sam laminde taki fahintar shi sai ma kokarin kiran mahaifiyar shi takeyi ta sheda mata cewa bai rabu da yarinyar ba, ashe, Hakan yasa yabar gurin cikin bacin rai batare da ya tsaya fada wa maryam zai wuce ba, Safiya wace tun dawowan su jiya gurin friends day, Ta fuskan kawar ta,na cikin damuwa, amma batason agane, Itakuma bawai sun samu lokacin kebewa da ita ba ce, Saboda haka yau da suka gama sa abinci a cikin take aways suka gyara inda sukayi aiki, Sai sukayo wanka kafin a tafi daurin aure, don da andawo guri zai cikia ne, da jama,a, Bayan sunan da shirya suna zaune su biyu a dakin maryam, Safiya ta dan kali maryam wace tadan kurawa wani kwali ido kamar mai karatu, Amma kallo daya zakai mata ka fahici ba wi kwalin take kallo ba a zahiri, Tadan jima tana kallon maryam ahakanan tare da tunanen may ke faruwa da maryam din hakana wai, Daga jiya zuwa yau ? Ganin bazata daina wanan tunanen ba yasa safiya dan taba maryam, din wacce tai furgigit, cikin dan firgita, Firgigit tayi alaman dawowa daga hayacin ta, sai yar ajiyar zuciya da take sakewa, Wanda hakan yakara sa safiya kara kallon ta da kyau, ta ko hango tashin hankali a tare da maryam din, Safiya tadan marairaice muryan ta tace maryam, wai make damun ki ne tun jiya fa na fanci kina cikin wani yanayi, Kallon safiya maryam tayi kamar kartai magana saidai kuma tace, Bari safiya ina cikin damuwa, tun jiya wallahi, jiya bayan zuwan mu gurin taron nan, Sai A,A yaga table din wasu mata da alamar yan uwan shine safiya, Yace min yana zuwa yatafi gurin su, sundade suna magana dashi sai suka batmr holl din gaba dayan su har shi, Ban kara ganin shi ba,sai text da yayo min cewa wai in bi Anty zuwa gida bai,samun dawowa kaini gida, Shine har zuwa yau din bai kirani ba baikuma yo min koda text bane, Nan kuma ta kwashe yadda akayi lokacin da taje gidan su gaida mahaifiyar shi, Safiya da ta gama sauraren maryam tai ajiyan zuciya, Tadan riko hannun maryam tace gaskiya maryam kina cikin tsaka mai wuya, Amma dai kiyi hakkuri pls kada ki sa wanan maganar a ranki, Ita mahaifiyar shi da take fadin haka danta yafi ki ne,? In,badon so ba may zakiyi da shi maryam,tuna duk inda aje son mace da tsari kin kai harkin zarta, Maryam tace wallahi Safiya ina son A,A shima yana so na, Matsalar mudai itace mahaifiyar shi yanzu, don ga yadda naji kalaman ta sam bata ra,ayina dashi, Safiya tace wallahi maryam kamar yadda anty tace din,nan haka zaki dake dashi kiga gudun shi, Yace yafasa mana yagani in baisha mamaki ba don dama ahi ya tare wa mutane guri, Maryam tace nidai safiya kin san cewa bazan nuna mai cewa naji maganar da sukayi da mahaifiyar shi ba sai in shi ya gwada min wani alama daga haka, Amma bari mu gani in har bai kiraki ba yau tau tabbas sunci karfin shi ke nan, Idan har bamu ganshi ba yau tun da kince yau ce ranan zuwan shigurin ki da ma, Yau wa safiya wallahi har naji dan sanyi daduk na rasa abinyi Gaskiya naji dadin wanan shawarar da kika bani har wani dan sanyi ya ratsa zuciya na, Safiya ta mike tajawo jakar kayanta da tazo dashi tana kokarin ciro kayan da zata sa, Shiga ce ta dinkin shadda gezena fara kal, yayi Saidaukar ido shaddan keyi irin dinkin yan Mali, akaiwa shaddan, Agogon shi kawai zai fadama cewa akwai shegun agurin , Wata hulla da ta,shiga da kayan yasa mai kyau da ita sai kuma wasu takalma, yan company, BELLA, yasa a kafar shi Kamshi dai ba,a maganar shi don yasa turare sunakai kala, biyar, alokaci guda, Kudi ya dauko yan dubu, dubu da yan dari biyar biyar yasa a kowani aljihun rigar shi, Motar da yashigo da ita tunda yazo bai shigeta ba tana aje, Itace yashigo yau zuwa gidan su KB inda za,a dunguma zuwa daurin aure, Jama,a sun ciki gurin makil, ana jiran motocin da za,a kwashe su, Sauran motocin da yashigo dasu yasa aka kwaso, akadinga dibar jama,a zuwa gurin, Duk wani abinda sharia ya tanadar gamay da daurin aure an gabatar a gurin a,lokacin, Joseph da tunda yake baitaba zuwa daurin auren musulmai ba sai wanan karon sai abin tazama mai sabon al,amari, Yaji duk abinda akeyi ya burge shi don komai a cikin tsari da kwanciyar hankali akeyin shi, Tunanen farko da yafara yi a ran shi shine, may kesa musulumai suna kashe auren su dayawa haka Dik da irin wanan, dokokin da akebi kafina mallakama mace, Idan har zai iya tunawa yadda yaji KB nahiran abinda yakashe akan wanan bukn to bai kamata kalman saki ya shigo ga auren yaran musulmai ba, Don yasan cewa musulunci batada banbancin al,ada, Da mai kudi da tallaka duk abuguda za,ayi agurin auren su, Hannu shi yadan daga ya shafi fuskan shi da yakeji kamar yawan jama,a yasa shi jin zufa agurin, Sai alokacin yadaga kai yakalli irin yawan al,umman da aka tara agurin wai duk akan auren KB wanda yasani, Jin ance fatiha yaga kowa na shafawa shima yadda yaga anyi yayi yashafa atare da kowa, Tare da Jibrin da kb da sauran abokai,suka mike inda maroka suka biyo su caaaa nan suka fara zuba masu kudi, Gidan Anty Dije akawuce don kwasan kayan abincin da za ai reception da shi awani katafare hotel mai suna NOMA FAMILY'S MOTTELS,,,, Gurin yai mugun tsaruwa sosai anan suka kama guri, don haka duk kusan matasan da suka hakarci gurin sun isa Noma motels Anci ansha komai yawadatar da jama,a sam,barka a gurin, Sai shirin yin Dinners wanda za,a yi da karfe hudu na marancen ranan, Maryam dake takure tun safe tana zullumin shawaran da sukayi ita da kawar ta, Sai kawai taji kiran A,A yashigo mata alokacin cikin wata kasallaliyar murya yake mata magana cewa, Bai samu kiran ta yadan yi tafiya ne zuwa mariga, shida wani kanin mahaifin shi, Amma zai zo su tafi gurin dina tare zuwa anjima in ya shirya, Bayan sunyi sallama, da shi takalli inda safiya take ta na mai yin ajiyar zuciya alokacin, Don da dabai bugoba tadauka cewa tayi missing din A,A dinta ke nan Wanan dinner ya hadu sosai don anyi abubuwan da yakamata agurin Maryam da A,A dinta sukan kebe a waje gurin wasu Flowers da aka shuka agurin Yadan kalle ta cikin kulawa yana mai shafan kanshi, Sai alokacin Maryam ta gano yayi wata yar rama akwanankin nan so sai don agaskiya ba haka yake ba da, Gabanta yafadi damm tace a ranta kodai saboda fitinar magabar sune yasa shi ramay wa haka, A,A ne yadan kauda shirun da cewa, maryam ina fatan bakiyi fushi ba jiya dana barki ko, Wallahi wasu yan matsaloline sukadan sani nadan fita daniyar inje in dawo sai kuma ban gama da wuri ba, Dan shiru sukayi alokaci daya shiko yana sauraren ta ne ko, akwai abinda zatace, da shi, Amma sai kawai yaga tayi shiru, bata da alamun zatai magana, Maryam shirun ki wani lokaci nasan maganace kawai, Ki daure ki fada min may ke faruwa ne naga fuskan ki da akwai alamar damuwa acikin ta, Shiru tayi kamar baza tai magana ba amma kuma sai ta yar nisa kadan, tace, Malam shin akwai maganar mu kuwa ko dai da matsala aciki, Ita kanta batasan lokacin da wanan maganar yafito mata abaki ba, Shiko A,A saida yadan razana aran shi yace kodai wani yafadawa maryam abinda ake ciki ne shida mahaifiyar shi, A hankali ya kira sunan maryam din ta dan dago kanta ta,kalle shi sai takawar da sauri, Yace ma kika ga ni har zaki ce hakan, Kai tadan girgiza mai alamar a,a ba komai, Maryam ki daure ki fada min dan Allah may kika gani har ki ce haka, Joseph wanda alokacin yadan fitowaje daga cikin hall din da ake taron, Don yadan amsa call din wani yauron shi dake kiran shi can wani sabon depot da aka bude, Waya yake yi da Chukuma, kamar ance yadaga indon shi sai hango A,A da maryam a tsaye gurin wa yan,nan furan,nin suna zuba hirar su ta soyayya, Kallo guda yai masu ya kauda kai garesu yana mai ci gaba da wayan shi, Saida yagama wayar da Chokuma ne har zai koma cikin holl din sai kuma idon shi ya kara sauka inda suke tsaye, A cikin zuciyar shi yace wanan yarinyar itace har ta isa fira da saurayi haka, Haba is too early ma, Yai yar tsuki ya shige ciki abin,shi don bai iya ganin, takaici, Yarinya kamar ustaziya amma ta iya abubuwan da bai kamata ba da dama, Itace hawan mashin yau kuma harda hira, Daidai lokacin da yake kokarin juyawa ne idon maryam ya sauka gareshi, Inda takalla malam A,A yabi da kallo sai bayan Joseph din kawai yagani yana kokarin shigewa cikin hall din, Maryam tsakanin mu ba dake yanzu yakamata mu fahinci junar mu sosai fiye da da, Nayi alkawarin bazan taba auren macen da ba tsarina ba, Ko kuma wace batada Qualities din abin danake so daga mace, Ra,ayinane in auri mace, mai sirin,classic, atare da ita, Wanda nasan cewa ta tara duk abin da nake muradi, Bakowane zai iya hangowanan abin ba sai namiji mai irin ra,ayina, So ki fada min ra,ayinki agamay dani pls, kada kuma kiji kunyar gayamin gaskiyar ki , Duk da nasan bazaki iya ki kalleni ki fada min kai tsaye komay ke acikin, zuciyar ki ba, Magan ganun da A,A yai ta zuba ma gwaunatin shi don yaga yakarawa maryam karfin son shi komai wuya komai ritsi, Maryam har mamaki yabata don jin yadda yatakarkare yana kokarin boye mata gaskiya, Gashi ita kuma ta kasa fada mashi cewa taji maganar mahaiyar shi aranan Yaya ma zata kalle shi, tace mai hakana don tasan zai ji mugun nauyin hakan, Akarshe dai sai cewa tayi kasan aure nufin,Allah ne mallam, in Allah yakaddara hakan nafi kowa farin ciki da hakan,,,,,,,,, Zaune yake tsakiyar saman gadon shi yayi dadaya da wasu takardu yana dibawa, Abinda yafado mai alokacin sai irin yadda yaji, masu daura auren KB nayi wa juna alkawari, Gyara zaman shi yayi yanamai tuna yadda yaga ana yawan cewa wai ai wani ya saki matar shi, Ko kuma yadda yaji mutum na alkawarin cewa ya dauki nauyin ci da sha da suturan matar shi amma sa kaga matan gasunan a wahalce,suna wahala, Kayan dake watse saman gadon ya dan har,hada saboda yagaji da aikin dayakeyi tun dazu, Yana shirin shiga cikin bathroom don yadan watsa ruwa yana son zuwa club gurin wani mutum, Wayan shi dake yashe a gefen filo, ce tai kara cewa, ana kiran shi Dawowa yayi yadauki wayar nobar wanda yagani yana kiran shi, yasa shi saurin daga wayar shi, Muryan Abdullsamada ce cikin wata irin sallama , yana cewa ya kake Joseph Yana cewa baida kudi a,wayan shi da zai ishe shi yai maganar da yake son yi, Amma ga Ibrahim nan Dan shi zuwa gurin shi daga haka wayar ta mutu dip, Alamar kudin nashi sun kare,ke,nan, tausayin mutumin yakama shi sosai, A ranshi yace,, may yasa wanan mutumin ke wanan wahalar haka, nan ya tuna da sanin da yai mai ada suna yara, Manya,manyar shaguna gare shi guda biyu, tab da kaya yana bada sari da kuma sayarwa cikin fararshi mai sauki Tunawa da yayi dattijon yace mai yaron shi ai zo gurin shi , Baisan ko yaushe bane zaizo don haka wayar ya dauka yakara kiran Abdulsamad din, Nan dai ya sheda mai cewa, yaron wajen shi ne ya ce kan cewa zaizo gurin Joseph din, Sai zuwa,safe yaron iso inda Joseph din ya tura azo mai dashi, Ibrahim yaro matashi dan kimanin ashirin da haihuwa, kamili ne mai rikon addini, Nan Joseph ya barshi har zuwa lokacin, da zai samu inda yasa shi cikin sana,ar shi, In gari ya waye Ibrahim zai tafi wani massalaci mai nisa can kasan unguwar su, Idan ya dawo kuma ,zai tsaya yadinga tillawa har zuwa wayewan gari, Gashi da ladabi don har yan aiki yana basu girma sosai,, Joseph a hankali yake kiwon halin Ibrahim don ya gwada shi yagani, Idan kuma gurin abinci ne baida tsanda ko ra,ayi kamar wasu yara duk abin da aka bashi ,zai karba, Sai wata rana Joseph yana daga ciki, sai ya dinga jin maman Choima tana fada tun yana sama yadan fara saukowa zuwa inda take. Don jin komay ke faruwa,take fada haka sai ya iske da Ibrahim ne take masifa, Wai,duk lokacin da sukayi abinci suka bashi sai bai cin nama yadawo masu dashi, Joseph ya,dago kai a hankali, ya kalli Ibrahim, wanda ke tsaye gefe kan shi kasa, Ibrahim may yasa kake haka inji Joseph, ? Ibrahim wanda yadan gyara tsatin shi cikin ladabi yace , Brother bawai ina masu wulakanci bane, saboda addini na ya haramta min cin naman da ba musullumi dan uwana ya yanka ba, Shiru Joseph yayi yana kallon Ibrahim yaro karami da,wanan akidar, acikin zuciyar shi, Maman choima dake jiran taji Joseph yai mai cin mutunci don ita tana ganin rainin wayo yai masu, Ji tayi Joseph yace idan abincin bai kwanta makaba arai zan dinga baka kudi kana zuwa gurin musulmai kana siya inaga zaifi, Aiko nan tsohuwa tahau fada cewa ya daure mai gindin yai madu wulakanci, Yakoma inda yafito mana waya kirashi da yazo zai ma mutane wulakanci, Joseph yace cikin wata murya ta warning ma,ma stop dat pls,,,, Maman ta wuce cikin kitchen, tana kallon naman,tana jujuya shi a, hankali,.tana masifa,,,,,,,,,,, ZEEE MAKAWA [2/21, 9:16 AM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Tafe yake cikin motar shi baka mai kama da siffan wani kifin ruwa, motar bakace wulk da ita, Yana rataye da yar suit shi a gefen kafadar shi sai hannu yake sawa yana dan sa,sau,ta nicktie, din shi, dake makale a wuyar shi, Air freshness yake son ya dauko ya, dan kara fesawa motar shi don shi al,a,dar shi ce sa kamshi duk inda yake, Dan save din motar yajawo daniyar dauko dan kwalban dake dauke da ruwan, freshness din, Wasu takardu suka fado daga gurin da yajo kwalban, Takardun da ya manta tun shekaran jiya ne a motar shi, Ibrahim yake son ya ba ya cika wani form, da yake son ya,je gurin computer training, A gagauce yadan fesa kamshin, sanan yajawo takardun ya aje a gefen shi ta yadda zai iya tunawa,don kada ya manta, Bayan ya Parker motar shi, yafito a,gajeyi don tun safe suke vurin wani taro da,akayi, Da takardun a hannun shi ya wuce zuwa dakin Ibrahim, Har yasa hannu zai tura kofar dakin, sai muryan yaron yani yana rera katun alkur,ani mai girma cikin wata irin murya maidadin sauraro, Maimakon ya shiga sai yadan tsaya har nakamar minti biyar yana da yaron ke fidda,harufan ya da ya dace a cikin natsuwa, Juyawa yayi yakoma hanyar cikin gida don ba zaiso ya katse mai karatun dhi Tunda bai san lokacin da ya farawar ba, balle kuma ya katse shi, A,hankali ya tura kofan falon ba kowa aciki a lokacin sai TV dake ta aiki, shi kadai Tashan wasu Christos ne wai peace TV, rawa suke kwasa da i,ho,ce,i,hoce, Wani iri yaji aran sa kawai sai yaji haushin su ,daukan remote din yayi ya kashe TV, A hankali ya fara tafiya a saman steps din da zai sada shi da bangaren shi sama, A kusan hawan karshe maman Choima tafito saye da wani dogon riga kanta daure da dankwali ta tsuke shi tam, Tace wa Joseph, So, you, are back,? You na welcome, wooo, Thank u mama, Your food don ready since, Cikin wanan turancin may kama da yare ta dinga jefo mai magana tanayi tana hadawa da,harshen IBO din, Ruwa ya watsa sai a lokacin yadan ji zuciyar shi tadan rage mai suyar da bai san dalilin yin ta ba, Yaso ya koma gurin Ibrahim don yai mai bayani amma sai kuma ya kasa saboda gajiyar da ya kwaso,, Don haka baima,sauko kasaba kamar yadda yasaba, indan yadawo yakan je gurin mama su dan yi hira, Don kawar mata da zaman kadaici duk da yasan Ejoma tana iya kokarin ta da yar tsohuwar, Washegari, musalin karfe takwas na safe, Joseph yasamu ya sauko tare da takardun Ibrahim na jiya a hannun shi, Dakin nashi ya nufa don yakai mai yasamu ya cika idan zai fita yau sai ya tafi dasu ya mayar, Tun daga yar hanyar da zata sadaka da dakin Ibrahim zaka ji muryan shi rarara, yana karanta suratul Maryam, Jin maryam mu da yake ambata aciki yasa Joseph tsayawa guri guda cif, Yace a hankali maryam in ,Qur'an, ? Ji kawai yayi yai kundunbale fadawa dakin yaga may yaron keyi haka, Ibrahim wanda ke zaune kamar a tsugune can wani dan sakon gado yana rike da Qur'an din shi yana mai karantawa, Jin kamshin turaren Joseph dayayi a dakin yasa shi dan bude indon shi da suke a lumshe, Don ya tabbatar da kamshin da hancin shi ya shako mai na Joseph din shine agaban shi ,ko,kuwa,? In ko har shi din ne to ko jiya ma da,dare da ya jiwo wanan kamshi tabbas shi din ne a gurin duk da bai bude ido yatabatar da hakan ba, Daidai ya kai A,ya" yadan dakata kadan yana mai cewa Sadakallahul,Azeen, Ina kwana yai mai acikin yaren su na IBO, Joseph ya dan daga mai hannu yana mai cewa,sorry for disturb pls, Takardun ya mika mai yace mai, ya cikia inda bai gane ba yasa may shi yai mai bayani, Daga haka yajuya kawai yabar dakin yana jin wani irin abu kamar kasala tana lu,lube shi, Sai zakakkan muryam Ibrahim ke mai yawo a kunuwa shi kamar a ciki yake wanan karatun,. Lumshe idon shi yayi yabi bayan kujerar da yake zaune yadan kwanta,, A hankali maryam ta ajiye, plate din da ta debo abinci, agaban Anty nata, Wacce ke kwance saman dogon kujerar da ke cikin falon nasu, Anty Dije tadan dago kai kadan ta kalli maryam wace ke kokarin juyawa don komawa dauko ma yar nata ruwan sha,,, Cikin murya ta wanda je jin jiki Anty tace wa maryam , Maryam ba,zan iya cin wanan abincin ba don sam bakina bai min dadi wallahi, Cikin dan marairaice murya Maryam tace anty dan Allah ko kadan ne kidaure ki danci, zaifi rashin cin da bakya, son yi, Da taimakon maryam Anty Dije tadanci abincin kusan spoon, hudu, gana biyar ta mayar tana mai cewa ta koshi, Bazata iya karawa ba haka don ji take tankar zata amaye dan wanda taci, Gudun kada tai amai Maryam ta kyale yar nata tana mai tatara plate din zuwa kitchen, Ido Anty tabi maryam dashi tana mai jin dadin irin kaunar da yar uwar nata ke yawan nuna mata ita da yaran ta, Ringing Tone din wayar Anty Dije ne ya karade gidan nasu a lokacin, Da sauri maryam ta isa inda,wayan take tana ruri, don ganin mai kiran yar uwar nata, Yusuf Joseph tagani baro,baro a screen din wayar, Kurawa wayar ido tayi har saida ya katse don kan shi, A hankali Anty tadan dago kai daga inda take, kwance tana son tasan kowaye ke kiranta ya katse, Don tana,son kaunar nata ta fada mata kowaye a layin,ke,kiranta, Tana kokarin aje wayar ne wani kiran nashi yakara shigowa again Dole ta nufi inda Anty take kwance, da hannu take mata tambayar waye akan layin, Joseph tace tana kokarin kara mata wayan a kunen ta, Da hannu taimata alamar, ta dauka kawai sai ta maida kanta saman hannun kujer a hankali, Cikin muryan mai,kama da ta maijin kasala take magana, Hello, ina wuni ? Mai wayar batada lafiya , Juses crisis, Dif maryam tayi tana mai cewa wa,iyazu,billlah, Jitayi tankar ta aje wayan do haushi, Sai jin shi tayi yana cewa may yasa may ta haka, Zazzabine ke damun ta yau kwana biyu ke nan, Jin wa,iyazu,billah da tafada dazu yadan sosai mai rai don yasan kalmace ta nuna wani tsari ga tsanar, abu, Don haka yanzu sai yadan gyara harshen shi da cewa ayya sorry fa ina gaisheta pls anjima zan bugo mata, Kagin ma ya kashe har maryam ta kashe wayar bin wayar yayi da kallo, Sai mamaki kuma yake a ran shi cewa may yasa musulmai ba su iya boye felling din su in suka ji an ance Juses,a gaban su, Maryam ko a hankali ta juyo gurin Anty tana fada mata abinda yace mata, Yinin ranan duk a kwance anty ta ti shi saboda yanayin jikin ta duk ba dadi, Ganin tana wahala da yawa yasa maryam bugawa yaya illiya waya tana sheda mai abinda ke faruwa xa yar uwar nata, Wace duk kwanakin nan akwance take bata jin dadin jikin ta, Ga wani amai dake zo mata yanzu duk abinda taci sai ta fitar dashi koda ruwa ne, Hakalin Maryam ya tashi sosai cikin dare da Joseph yabugo muryan ta kamar na mai kuka take mai magana, Tana sheda mai yadda ciwon ke matsawa yar uwan ta yanzu sosai, Shiru yadan yi nawani lokaci har maryam din na,,zaton ko cewa ya kashe wayan ne, Tace cikin siririyar murya, hello,, Yace ina jinki kunje asibiti, ta girgiza kanta alokacin kamar yana ganin ta tace a,a Saidai zuwa gobe insha Allah zamu tafi yaya yau ya bugo waya yake cewa mutafi goben, Ok to barin yi magana da shi Illiya din tukun 'I will call you back,,, Ok tau nagode tace tana mai kokarin aje wayar a lokacin shikuma yana mai ce mata ina Assalam yana lafiya ko? Cikin kosawa da yin wayar tace mai yana lafiya sai anjima, Itace kuma still dai ta,katse wayar kamar yadda ta yi dazu Yai shiru yana dan mamakin irin halin Maryam na rashi son mutane Yasaki ajiyar zuciya yana mai kara nazarin ta, Tuna wa yayi da zancen kiran illiya don haka nobar shi ce ya kira,, Bayan sun gaisane yai mai jajen ciwon matar shi sai, ya,kecewa Dama ya bugo waya ne don ya tambaye shi ko yana iya tura mai doctor lawal yadiba matarshi Don yadda akace mai tana jin jikin har ta kasa daukar waya daya kirata, Ya, illiya yai murna kwarai da wanan taimakon da Joseph yai mai na turawa har gida a diba mai matar shi, Saida Doctor Lawal ya iso gidan sanan Joseph yakira yake sheda masu cewa gashi nan shigowa, Mamaki ne yakama maryam sosai don ganin cewa yasan yadda shari,ar musulunci yace ayi, Am.a kuma da,tai tunane saitaga babu mamaki don yana tare da su jibrin yau da gobe dole yasan komai, An mata allurai dakuma yan magunguna, sai fitsarin ta da akace akai gobe, Bayan fitar doctor dakamar yan min tina sai,gashi ya kara kira yana tambayar ta Ta girgiza kai tace ban san may doctor yace ba yadai mata allura, Nan yai mata sada safe yana mai jaddada mata cewa ta tabbatar da cewa Anty tana shan maganin ta, Joseph yaso ya shivo saidai yana tsoron irin masifar da tsohon shi ya za,zaga mai, Inda ya bashi umurni da cewa indan har bashi yace yana son yazo ba kada ya fara yashigo garin kwantagora, Tunda badon su ya haife shi ba da zai dinga kashe masu kudin shi abanza hakana, Fada sosai yaiwa Dan nashi lokacin bukin KB da sukayi inda labarin komi yazo kunen Mr Ema din a lokacin ne yai kamar zai daki Joseph din don haushi, Jikin Joseph a sanyaye don badamar zuwa yadiba halin da Anty nashi ke ciki, don gudun masifar mahaifin shi wanda sam bai son hurdan shi da yaran varin da yake amfana dasu, Hannu yasa yadan shafo sanjen fuskan shi da ya kwanta mai lub a fuskan, Ya furzar da yar iska mai dan dumi daga bakin shi, Ibrahim ne yafado mai arai don haka yatadashi inda yai mai shatar mota zuwa kwantagora da kayan dubiya irin ta marasa lafiya, Anty Dije tayi mamaki kwarai da irin kayan da Joseph ya bayar ,akawo mata tundaga Lagos har KG, Lemo, Abarba, Ayyaba, Apple, kwakwa, carrot, water millow, pears, da,sauran su bar manja da garin can saida ya siya mata, Waya anty tasa aka bugawa Joseph tana son tsi mai godiya na taimakon da yai mata, ga likita ga kayan marmari, da yayo mata, Likita ya tabbatar da cewa Anty Dije tana dauke da shigar ciki na wata biyu da da kwanaki, Maryam tafi kowa murna da wanan labarin cikin, wanda har uwar mijin ta tafara zance wai ya karo mata tunda anty tabar haihuwa, Da sun dan samu matsala dasu yanzu zasu fara mata gorin taki haihuwa kuma ta hana auri wata,,,, ZEEE MAKAWA [2/21, 9:16 AM] ‪+234 806 595 8685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 2⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Yan uwa musulumai ina mika gaisuwa gare ku ,akan wa yan nan yaran makaranta yan garin misau da ke cikin jahar Bauchi da suka samu harin mota ta hanyar su zuwa kano ziyarar Arewa 24,wanan satin da yagabata suka mutu su ashirin ta re da malaman su,, Masoya TAKARI novel da FUREN JUJI ina fatan za muyi masu adduan fatan samun Rahamar ubangiji, tare da mika ta,aziyar mu ga yan,uwa, da, iyayyen wa,yan nan yara, Allah ubangiji kasa Aljannan Fiddausi tazama makomar su,👏👏👏👏 Mahaifin , Ibrahim Abdulsamad, yaji dadin yada yaga dan shi ya koma cikin dan kankanin lokaci, Bakamar yadda suke zube a cikin gari ba da babu mataimaki, Babu wanda ma yasan cewa suna cikin wani halin bukata na rashin yan uwa da galihu, Yana ji yana gani matar shi ta gudu mai da yan shi mata, zuwa kasan su, Wanda bakomai yasa shi kyaleta dasu ba sai tsabar yawan talauci dake cin shi, Ki abinda zasu ci tunda yai gobara shagunar shi suka kone kurmus, Amma sai yara,daya daga cikin musulmai wanda zai taimaka mai da wani abin, Gashi har zuwa yanzu yan uwan shi na da suna kawo mai tayi akan ya koma akidar shi tafarko, Babu komai acikin wanan sabuwar akudar da yadauko, illa wahala, Dariya kawai yakan masu yabasu amsar cewa shi yabar su ke nan har abada Bazai kara dawowa cikin banyar bata ba saidai ya mutu a hakan, Girman da yaran shi suka farayi ne yadan rage mai wahalar don suna zuwa yin dako a bakin kasuwa sukawo dan abin da suka samu ayini asarrafa, Ko shi Ibrahim saida bukin KB da akayi ne yasan cewa suna da alaka da Joseph,, Lokacin da yaga irin yadda Joseph ke yi agurin yazo yana fadawa mahaifinshi cewa baisan cewa IBO bane saida yaji yana yare acikin waya, Abdulsamad yai dariya inda yakewa diyan shi bayanin ko ya suke da Joseph, Nan ne ibrahim yace zai je gurin shi ya ziyar ce shi yagani ko za,a samu wani cigaba anan, Maihaifin na Ibrahim baiki ba don yasan kowaye Joseph zai iya taimama wa ibrahim din, Sai ko gsshi cikin ikon Allah ibrahim din yazo cikin kamata alheri don bai taba zaton cewa yaron zai can za cikin dan lokaci guda haka ba, Ga sakon kudi har dubu hamsin anbashi yakawo wa mahaifin shi tare da tsaraba, Kwanan shi biyu da zuwa inda yakoma shedawa Anty Dije zai koma, Sako tabayar akai ma Joseph din wani robber da akai sild din shi Sai kuma kilishi cikin envelop, mai yawa cikin wani babban leda tace Ibrahim yakai wa Joseph, Bakaramin mamaki Joseph yayi ba lokacin da Ibrahim yagabatar mai da sokon da Anty Dije ta aiko mai dasu, Dambun nama ne cike a roban sai kuma kilishi mai yawa, Daga kilishin har Danbun Joseph yarasa wani yafi dadi daga ciki, Sai mamaki yakeyi yana kada kai cikin jin nauyi, kamar a gaban anty din yake, Shi yana gani kamar ta ksshe kudin da yakai dubu dari akan wanan abin, Bai daga daga gurin ba sai da ya kira ta acikin waya yana mata godiya daga karshe ma yarasa may zai ce mata, Mamaki kwarai anty tayi don jin yadda yake zabga mata godiya akan dan abinda baikai yakawo ba, Shida ta lodo mata tsaraba har saida ta ba makwabta da kuma gidajen su ita da mijin ta, Amma,shi gashi ko dubu ashirin bata kashe mai ba yata zabga godiya, Shin shi Joseph din nan wani irin zuciya gare shi ne wai gashi da bawai, yasan kaidar zumunci ba ne a ddini, Amma yarike ta tam kamar wata yar uwar sa ta ji, Ita dai fatan ta dai,akullun Allah ya kebo Joseph, yadawo cikin Islam's, A hankali Joseph ya maida tsarabar anty wani abincin shi na daban koda yaushe yana amfani da abinshi kadan kadan, Wani irin gurnani take yi wanda har a fili zaka iya jin yadda takeyi wanan karar, Joseph dake shirin hawa sama yagama kallon national news, a TVC, Da sauri yai hanyar dakin na maman choima wace ke faman wani irin Gumza takar ana shirin yankar ta, Da karfi Joseph da Ejoma ke kokarim daga ta daga kwanciyar da tayi tana fidda wanan sautin, Cikin wani irin kara tabude idon ta tana mai cewa Joseph's da karfi, Firgigit take kallon su da sauri ta rugumo Joseph din daga jikin ta,, Sai kuma ta fashe dawani irin kuka tana magana maiban tausayi, cikin kuka, Tana mai cewa,Joseph they want to carry u away from us,woooo, Joseph da ya rungumo tsohuwar zuwa cikin jikin shi, yace mata sowaye, Cikin kuka tace bata san su ba amma tana yawan gani su,,a tare dashi acikin su,, koyaushe, Sai yaune babban su ya ce har da ita zai wuce in,har tana rike shi, Shine wanan gumzar da take tayi cikin barcin ta da ihun da take ta kwasa yanzu, Joseph yadan tallabo kan kakar tashi, zuwa jikin shi yana mai lalashin ta Tunda yaga cewa tadan kwantar da hankalinta yasamu ya sata kwantawa don ko zata samu barci, Yamike zuwa dakin shi jiki a sanyaye, zuciyar fam da tunane kala kala, Ashe haka wanan yar tsohuwar ke wahala idan tace mai tayi wanan mafarkin,, Hankali shi yatashi matuka yana tunanen may ke shirin samun shine haka, Washegari, tunda safe Joseph yabar gida zuwa gidan wani babban pastor da ke zaune a cikin Lagos, Saidai bayan bayanin da Joseph yai mai sai ya umarci da azo mai da wnan tsohuwae wurin shi Joseph yakoma yazo da maman choima acikin shirinta na irin manyan matan IBO, Pasto ya riko hannun mama zuwa yan wasu lokota, Can sai ya sake yadan daga kai yana mai kallon Joseph wanda ke zaune gefen su saman wata far kujera, yana mai rike habar shi da hannu guda yana dan shafa, gemun shi, Idon da pastor yadan tsura mai baisa Joseph ya canza daga yadda yake zaune ba tun farko, Pastor yadan kada kan shi yai yar gyarar murya wanda yasa duk suka kura mai ido, Don jin irin bayanin da zai masu gamay da mafarkin da takeyi, Mama inji pastor kada ki damu wanwn bawani abin damuwa bane danki zai zama wani abu ne nan gaba shiyasa kike ganin wan nan abin, Amma,zai bata holy water wanda zata dinga wanke fuskan ta dashi har zuwa sati, Idan ta kara wanan mafarki sai su dawo, duk kan su, Sukai godiya Joseph ya kawo kudi yabawa pastor pastor yaka da kan shi alamar aa ba,zai karba ba, Yace we are just send to help, the, neediest, Yai masu addu,a a baki dayan su inda sukai sallama dashi zuwa gida, Tun,daga wanan ranan maman choima ta fara amfani da ruwan holy water, kamar yadda pastor ya umurce ta tayi, Shiri yakeyi sosai saboda tunda safe yake son takama hanya zuwa kano don dibo wasu kaya da wani tsoho yai mashi tallan kayan company, Duk shirin da,Joseph keyi hankalin shi na gurin kakar shi wacce ta nuna batason zuwan shi garin kano sam, Saida ya gama,shirin tsab ya sauko cikin shigar kananin kaya, Kayan ya karbe shi sosai don ya fitar mai da surar shi tsab, Karfafan namiji mai duk wani siffa mai nuna karfi daga jikin da namiji Saidai Joseph ba mutum bane mai son magana don haka ko murmushi da wuya kaga yayi ta, kasafai, Guda guda yake tako hannu shi guda na acikin ajihun wandon shi guda kuma yana dauke da yar briefcase din shi, Direct saman kujerar da maman choima take zaune ya nufa inda shima yazauna gefen hannun kujerar, Yadan langabo kanshi zuwa saman kan maman Choima din, Mama ,I, gona miss u, wooo, Kamar yadda yasaba fada mata duk lokacin da zaiyi tafiya mai yar nisa, dasu, Cikin muryan da tanu cewa ta manyanta tafara magana,kamar haka, My child , god dey with u,for D whole time , u go spend there,,, Ejoma dake gefe ta amsa da fadin Ameen,, Joseph yamike tsaye yana dan gyara, wandon shi, tare da yi masu sallama, Motar da zaitafi da ita Ibrahim ke ta faman gogewa da kakabewa, Nan sukayi sallama da ibrahim din yabashi dan kudin da zai yi amfani dasu kafin yadawo, Adduan dayaron ke mai kullun tasashi jin dadin rayuwar shi aduk lokacin da uai mai ita, Ahankali ya furtawa ibrahim din da Ameen, tnxs brother, Yaja motar shi yai gaba yanama Ibrahim horn alamar bye,bye, Abamu na Allah da Annabi, A taimaki almajara sadaka saboda Allah, A,wani gidan mai daidai shiga garin kano, wasu almajirai ne suka baibaiye wata mota, da wani matashi acikin wani yaddi mai ruwa toka, Da sauri saurin ya ja glass din motar,shi sama saboda gudun kada su damay shi, A daidai lokacin Joseph ya parker tashi motar kusa da ta saurayin, Daga cikin motar shi yakewa saurayin kallon mamaki, Wata yar jagora wani tsohon makaho da, ta kurawa Joseph ido tun lokacin da ya tsayar da motar shi, Da kai yai mata alamar tazo ba bata lokaci tasake sandan dan tsohon makahon da take ja zuwa inda Joseph din yake, Dan Allah ki karbi wanan duk almajirin dake gurin nan ki bashi sadaka, Kafin yakara sa mika mata sai gawani dan dukaken mutum mai yar wani doro abaya ya iso gurin cikin sauri, Ataimaka ma almajiri da sadaka Alhaji, Malam haru, gashi yabamu yace duk wanda ke gurin abashi saboda Allah, Kafin minti biyu duk sun baibaye motar Joseph Alhaji yadda kai muna Allah yai maka Allah yasa agama da duniya lafiya, Wata yar tsohuwa da aka jawo duke a nanade cikin wani keken, turawa, Tace, Allah ya tsare Allah yabada sa,a Allah Allah yasa afi,haka arayuwa, Daidai lokacin mai zuba mai a motar ya gama zuba mai man da ake zubawa, Yaciro kudin shi ya mika mai, ji yayi ana gardama bada yaran almanirai masu bara ba, Yakara yafutu yaron dake tsaye cikin yagagun kaya gaban rigar a bude, robar baran shi duk tayi dauda Ya,mika mai kudi, sukai dubu biyar yace su raba aikuwa nan guri kaure da suratai, Shika har ya harba motar shi zuwa cikin gari don yasamu ya isa inda akai mai masaukin kwana, Kafin gobe, su tafi tsohuwar maikatar su diba abinda suke so aciki, su saya, Alhaji sabo, wani tsohon mai kudine wanda yasamu kariyar arziki Yanzu baida komai sai sayar da yan kaddarorin dake gare shi, yake akai kai don ya samu dan abinda, suka ci shi da iyalin shi, Yakira abokan sanar ashi sukai mutun biyar don su sai waban injin din amma sai suyi mai tayin tsiya ta yadda zai fadi warwas, Shine wani yaron shi na da dake lagos yai ma su Joseph talla ko za,su saye, suyi amfani da shi, Tun,cikin dare, da ya shigo Alhaji sabo ya zo har masaukin shi don su gana saboda in har yakai gobe Mahassadan shi na ita bata zancen su soke al,amari don ganin cewa bai farfado ba ko kadan, Bayan sun gaisa Alhaji Sabo yafadawa Joseph irin halin da yake ciki da kuma yadda makiyan shi suka sashi agaba don kada ya farfado, Joseph yai nazarin wanan bawan Allah sosai har yaji yana son ya tallafa mai, Dama da Sonny ne zasu sai wanan kayan suyi masana,an ta dashi can,Lagos din, Don haka sai yaba Alhaji sabo shawaran cewa, may zai hana ya canza sana,a yagani, Amma yabashi shawara ya tafi yai nazari akai, duk abin da ya gani yafada mai Kamar masu jira aiko tunda suka ga su Joseph tare da jibrin da KB dasuka iso kano aranan suka samay shi Sai aka fara zuwa gaisawa da su tamkar an san inda suka fito, Daganan aka fara tambayar ko daga wani gari suke, Wata irin masanan ta zasu yi ai ko yakamata sukira wa, yanda suka san kan injin su diba masu don gaskiya injin din ya dade, da, lalace, Tun nan Joseph yagane cewa agent, din mahassadan Alhaji Sabone, Ganin irin body guard din dake biye da Joseph da mutanen shi gashi kuma suna ta son yin suka amma ba fuska, Bayan sun gama dibawa Joseph yasa adibo mai enginers masu aikin kwarai daga lagos zasu biyu jirgi, su zo Su di mai kyau engine din idan baiyi mugun baci ba, Bayan Joseph yakoma masaukin shine yake ba su jibrin labarin hiran shi da Alhaji sabo, Gashi kuma sunga zahiri duk da bawai sun bada fuska ba a gun mutanen, Bayan ma,aikatar sunzo sun diba engine din sai suka tabbatar da cewa dan gyaran da za,ai mai kadan ne don komai nashi lafiya lau yae Kuma na,da ne mai kyau yanzu ba,a samun irin, shi so sai, Tausayin wanan bawan Allah Joseph yaji sosai sai yaga yakamata yai mai hanya, Shikuma Alhaji Sabo kamar yasan cewa Joseph na wani planing akan shi, Sai gashi ya gaiyaci Joseph har gidan shi gurin iyalin shi, Gidan ba, laifi baba ne amma, dai da alamar porvaty, aciki, Amma akwai addini, ga ladabi da sanin ya kamata atare da su, Wani dan karamin yaro a gidan yazo da sauri yadinga fito da butoci yana direwa agaban mutane, A, gaban Joseph yadire wani butan silver mai ruwan gold, Har zai wuce sai Joseph yajawo shi zuwa jikin shi yana tambayar shi sunan shi, Amma sai ya ce wa Joseph, barin muyi sallah kada mu makara sai in fada ma, Joseph yasake yaron yana mamaki yadda yara kanana suke iya akidar addini tun suna yara, Shin wai duk haka musullumai sukewa yaran sune tun suna kanana ko kuwa,, Murayan dan yaron ya katse Joseph din yana cewa uncle kayi alawala, kada mu makara mu tsaya baya kaji, ba kyau,, Joseph yai murmushi yace kayi kawai zan biyo ka a baya ina jiran wani ne, Sai yaji wani irin nauyi da kunyar hakan Tunda yake baitaba jin nauyi ba sai yau, dan karamin yaro na sa shi ahanya, Kafin su fito daga sallah Joseph yabar gidan, cikin yar damuwa, A can masaukin shi yana isa ya jefar da top din shi a saman kujerar dake dakin Gurin fridge yanufa yadauko goran ruwa ya ballemarfi ya kafa a abakin, shi sai roban duk ya kwakwade ruwan, cikin roba, Ya wurgat da roban can gefe guda saman gado yafada jagab, Sai kuma yakai kwance tabayan shi yana mai lunshe idon shi kamar mai barci, Ringing din wayar shi tasa shi bude idon shi, dake lunshe kusan yan mintina, A, cikin sauri yajawo wayar don kada kiran ya katse Nobar anty Dije ce ke kiranshi,bayan sun gaisa,dashine take sheda,mai cewa Asalam ne ke magana dashi, Yana karban wayan sai ce mai yaron yayi, uncle wai bazakazo gurin walimar saular su little mummy ba, Da farko baigane may yaron ke nufi ba, saidaga baya, Ya,fahinta da abin dayaron ke nufi, Anty Dije ce takarbi wayan take mai baya yadda akayi, Wai cewa yai Joseph din zaizo sai kace i, bazai zo ba, Tana fadin hakan kawai sai yagane cewa akwai abin da akace wa yaron agamay dashi,,,,, ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Duk, abinda ya kamata Joseph yayi ya aiwatar a kano, Don haka sai yai shirin komawa gida, A cikin dare, Sonny ya bugo mai waya cewa ya fi bukatar su aje wanan engine din a garin Abuja, Aboda haka yanzu dole Abuja Joseph zai ratse don neman gurin da zasu yi wanan aikin, Dashi da Jibrin ne ke ta faman yawon neman guri, inda ya kamata, Wani sabon side ne suka samu a NYanya, acan zasu yi wanan masana,antar, Tun da aja fara wanan aikin sau guda Joseph ya dan zo Lagos yaga su mama, Sam yafita duk wani zancen zuwa kwantagora yanzu saboda baida lokacin hakan bukatar shi kawai ya ga wanan masa,nantar yasamu kafuwa kamar yadda suke so, Ma,aikatar dake aikin gurin yau ma kamar kullun su halarra sun fara aiyukan su, Kwasam sai suka dinga jin wani irin ihu na tashi tankar mace na ihu tana neman taimako, Wasa wasa sai jin ihun sukeyi yana karuwa kafin kamar a inda suke, aiki karan ke, fitowa, sai gani sukayi wani irin iska mai karffi yana kada ganye da ciyawon dake gurin, Mutun daya daga cikin su yafara yar da abin digar da ke a hannun shi, Ya,arta ana,kare, ganin haka sauran ma,aikatar gurin suka fara, arcewa, kowa sai kwasan gudu yakeyi ba mai tsayawa jiran wani, Suna ji suna gani gurin ya gagare su aiki dole suka bido nobar jibrin wanda alokacin shima yana shirin zuwa diba su, Dariya ya fara yi lokacin da suke fada mzi yana ta faman kyalkyalar dariya Yana isowa ya shima yaji wanan sautin tun daga ne sa aiba girama,ba, arziki ya fada motar shi sai maida nunfashi guda guda yake yi, Sai da yatabbatar yabar unguwar ya dauko wayar shi ya buga ma Joseph, Kwance yake daga shi sai rigar barcin shi dark blue yana saye da wani dan gajeren wando, Kwance yake tare da Aisha ya rungumay ta, a cikin jikin shi sai kwasan barcin su sukeyi,Aishan, wacce ta shigo jiya da,dare, Dukkan su suna tare da gani kowan su nada gajiya atare da shi, Karar wayan da Jibrin shi da KB suke ta bugo mai a jere da juna yasa Joseph a hankali bude idon shi Hannun shi yamika saman side drower din shi inda wayar shi ke ta faman tsuwa, Saida yai yar tsuki alamar jin haushi kiran a wanan lokacin, A,llo, yace cikin lumsherwar ido, idon shi wanda ke cike tab da barci, alokacin, Cikin tashin hankali Jibrin ke magana man an samu matsala fa, Kai Jibrin wanan kira haka tun da safe, haba,haba kasan fa ina son hutu, Kai Baba anfa samu matsala sosai nake fada ma, New side ba lafiya fa, What's, Joseph wanda ya mike zubur daga kwanciyar da yake, Aisha ta dan yi kojarin rungumo shi ai bai san lokacin da ya ture taba gefe ya mike zaune, May kake son fada min ne Jibrin may ke faruwa ne wai,? Jibrin yace wallahi gurin sam baya shiguwa, saboda wani mugun sound da ke fitowa a cikin kasa, Juses crisis, inji Joseph Jibrin yace lalai dai kam kara fadi, Don nima daga can nake don na sauka cewa abin wasa ne dafarko, sai gashi naga abin ba dama wallahi, Bathroom ya fada don yadan watsa ruwa tunda ba maganar sallah gare shi, Cikin sauri ya shirya Aisha tana kwance cikin A,C yadan kalle ta ya kada kai yace Aisha kitashi kiyi sallah mana, Ban san may yasa bakya son yin sallah in time ba fa, Tai wani mika tana kara,shigewa cikin bargon dake saman ta, Tace, ai zan tashi yanzu, inyi na,gajine sosai wallahi Cikin sauri ya fesa turare a jikin shi yadauki wayoyin shi yasa a aljihun shi, Aguje yabar gurin, inda su Jibrin ke fada mai cewa sun na,nan ne ya,nufa, A bakin hanya yasamay su inda duk bayanin da suke mai sam bai dauka ba aranshi, Mota yashiga tare da wani William, suka nufi gurin, Tun a saman hanya suke jin wanan sautin tankar mace na kuka tana neman taimako, Bakin shi dauke da irin addu,oin su ya nufi gurin gadan gadan gadan, Wani irin matsanacin ihu yake ji tankar kunnuwar shi zasu tsage a lokacin, Sai kuma yaga kamar kasa na motsi, da girgizawa, Iska yafara ji yana gabato gurin da yake kamar za,a daga shi jin sautin na tankar yana motsowa inda yake yasa shi saurin dawo,wa baya a,hankali sai jin sautin yakeyi tankar kasa zai tsage, Hannu shi guda a cikin aljihu guda kuma yana rike da wayar shi, Dole ya dan hada gudu don kara girgiza kasan gurin ke yi, A mota yasamu Mr William, yana jiran shi, ba bata lokaci suka tada mota suka bar gurin kamar walkiya, William ne yake bashi shawara su je, gidan wani pastor, masaka su dauko shi Zowan pastor da mukar, raban shi yafi komai kara bata zancen don wani irin, Iskane yafara lailayewa yanagi sararim samaniya, gurin na baki, kamar hadari, Kwana biyu ana wana badakalar abu yaki tsayawa sai kara rikicewa duk mai maganin su na Christian an dauko amma abu yakiya, Jibrin ne yabada shawaran adauko, Abdul, mudallabi mai almajirai a gwada agani, Ta cikin waya suka buga ma malam waya suna son don Allah yazo ya taimaka masu, Malam din yace gaskiya bazai samu zuwa har Abuja ba yanzu, Ganin mallam zai kine yasa, KB yai ma wani kanin mahaifin shi waya aminin wani shehin malami malam Dahiru, tare da,wani malam Lawi,,, Allah ya taimaka suka ci karfin malam Abdulmudalabi, Sukazo tare gurin tun safe suka kamo hanya sai musalin, karfe biyun rana suka isa gurin, Kamar ko, yau she gurin na gumza kamar kullun, Malam tun isar su yafara cewa Allahu Akbar, Allahu,Akbar, Qur'an din shi dake cikin wata jakka da ya ratayo yadau ko, Tare da shimfida wani daddaduma mai laushi sai turare da yadan yayafa agurin, Suna sauran kusan makamanci yadda malam yayi sukayi, Suratul Suleiman su,ka,fara karan tawa,, Sai suka sauran ayoyi dake koran Aljannu, Kuka akeyi mai ban tausayi yanzu, malam da kan shi saida yai hawaye, idan yaji yadda abin ke wani gumza, Yadan dakatar da karatun da yakeyi yai gyarar murya, yana cewa, Macen ce ke wanan kukan saboda wai nan gidan su ne na kaka da kakan ni, Shine yanzu za,a zo ab kore su batare da sanin suba, to su bazasubar gurin ba, Saboda tayi sabon haihuwa har an fara taba mata diyanta,,,,, Joseph dake tsaye nisa kadan yace No mu ba.u san cewa tana gurin ba ,,aida bamu zo ba gakiya, Karatu malam yaci gaba dayi har wani lokaci, sannan suka ce zasu tafi masauki har zuwa gobe, Masauki mai kyau aka kai,su, inda har zuwa yanzu Joseph bawai ya yarda da zancen su malam bane tunda yaga pastor ma yayi yagaza, aganin shi aiduk guda ne, Sosai malam yatashi cikin dare yai aiki irin yadda yakamata har na tsawon kwana bakawai, Cikin daren na bakwai din ne, malam yakammala da su mazauna gurin na boye, Tunda safe suka shirya shida sauran malamai zuwa gurin da ake yin ma,aikatar, Kamar kullun saidai yau gumzar yarage so sai fiye da kullun, Sai iska ke kadawa kamar hadarin sabon damana, Su malam sai karatu suke zubawa , tamkar zasu tashi sama, Allahu Akbar, Kabiran Allah mai girma dadaukaka, Wani irin halitta ne kamar macijiya saidai sun ban banta agurin kai da maciji Yafito cikin wani rami da yaran shi zaban tsoro, duk wanda ke gurin, saida hankalin shi ya tashi, Hanyar gabas suka bi uwar na gaba ana wani irin kuka kamar na agwagwa, Saida suka gama wucewa ita da yaranta kaf. Sai ga wani shirgegen irin halittan Ashe wai shine, na mijin, su, shine yasa, ya tsaya baya, sai kuka sukeyi zabar tausayi, suka harba cikin daji, wani zugun kurmi dake gabas kowa na, kallon su wanda Allah yaba ikon zuwa kallo, Saida suka bace wa ganin mutane, sanan Joseph yai wa i irin ajiyar zuciya ya waiga inda malam,Abdullmudalabi yake yai yar murmushi mai kama da yake, Suko su malam sai kara cigaba da karatu sukeyi da kara neman wa gurin tsari, na har abada daga sauran ire,iren abun boye wa yan da bamu gani, Sosai Joseph mamakin irin wanan baiwar ta su malam yakama shi, Saidai kuma yaji muryan malam na cewa ai Alkur,ani maigirma baibar komai ba,, Don shi warakane tare da kuma kariya ga duk wani masifa, Malam yaci gaba da bayani cewa daga mutane dabboi da aljannu, duk suna amfana daga Alkur,ani mai girma, Bayani kala,kala, malam yai ta ma jama,an, dake zagaye da shi suna mamakin wanan ikon Allah,. Ranan Sonny yashigo Abuja wanda sai video, kawai na wanan al,ajabin yagani bai samu gani live ba, Yacewa Joseph inbadon harda shi yagani cikin video ba da sai yace bada gaske bane, Nan dai yakara tambayar, cewa ko anyiwa gurin addu,a sosai, Kyauta ma tsoka harda motocin shiga su malam suka dawo dashi akan wanan aikin, Shikadai ke cikin dakin shi saboda ya sallami Aisha badon taso wucewa shidai ne ya matsa mata da cewa takoma gida hakanan, Waya yake yi da maman Choima da Ejoma yana mai ba su, labarin irin abinda yafaru da su a can sabon gurin da suke aiki, Chaaay O there's God woooo, Joseph i, warn, u not to go there , but ,u refused, Dis, things go kill person wooo, Ranan saida takai shi church don aima spirit, din shi addau,a, Sosai yabawa baban shi labarin abinda yafaru da su tsab, Baban ne, yace mai ai irin wanan,aikin dama sai irin malaman din, nan, A ran shi yace So even Dad knows something about, dis malams, Tundaga wanan ranan Joseph tashiga wani hali acikin zuciyar shi, May yasa pastor yakasa yin wanan aikin da su malam sukayi, Ko yaushe al,amsrin musulmai is amazing, to him, Alhaji Sabo yazo har Abuja don yaiwa, su Joseph ja,je, abinda yafaru dasu,, Sunkai wani lokaci zaune tare da dan tsohon mai mutunci da kamala, Wanda, ba ruwan shi da,kowa sai al,amarin gaban shi kawai, Ana,gobe Alhaji Sabo zai koma Kano, Joseph ya shirya ystafi har masaukin dan Dadtijon, Inda yasamay shi yana sallah acikin wani irin natsuwa, Duk da ga girma ya kamashi amma sallah shi yakeyi hankali kwance, Zaune inda Joseph yake ya kurawa Alhaji sabo ido tamkar yau ya fara ganin ana sallah a rayuwar shi, Ganin shi bai sa tsohon yadakatar da sallah ba har sai zuwa lokacin da yakai iya adadin da yake bukatan, Sanan ya tsaya yashafa tare da jero kyawan adduoi, A hankali ya shafa addu,aan da ya idar a fuskan shi yana yin hamdallah, Sai lokacin ya wai,go inda Joseph, yake zaune, ,yana mai yi mai murmushi cikin kulawa, Sosai suka tatauna akan harkan business din kada watau cotton, wanda kowa yasan mutanen garin kwantagora da wanan sana,ar, Sosai Alhaji yai murna, saboda dama yadade ya son wanan sa,ar, ta kada watau, cotton ,, Tafe yake a motar shi yana kallon yada fitilun suka haska,ka titi, Abin yadaure mai kai sosai yaya,, za,a ce pastor ya kasa korar wanan abin sai malam, Gashi kuma shi malam din yace waida Alkura,ni mai girma suka yi wanan aikin, Wani irin ajiyar zuciya yasake don gane yadda al,amarin zancen yake, Batare da sani kowaba washe gari ranan jumma,a, da musalin shadayar rana, Joseph ya shirya yai shiga mai kyau da ma,ana ya kulle ko ina na gidan shi, Makullin motar shi ya sura, yajefa, ta a cikin, aljihu, rigar shi, Ta,fe yake a hankali. cikin motar shi duk tunane ya cika mai zuciyar shi fam Wani dan guri yasamu nisa da inda yaga jama,a suna ta taruwa, Saida ya tabbatar da komai ya kam,mala kamar yadfa yake bukata,, A,hankali ya fito ya kulle motar shi ya taka kamar kowa har zuwa cikin haraban, masallacin Watau Central Mosque, inda yaga gurin yaimai wani irin mugun cikafam, da al,ummar Annabi,,, Kowa sai abinda ke gaban shi yakeyi ba mai magana da wani wasu sallah wasu tasbihi,, Wani wanda yagani yana yawo da ani abu kamar tire yaiwa bayanin komai, Cikun dauki da zumudi mutumin yai wurin lima yana mai bayani shida sauran members din masallacin, A. Wani dan daki aka kai shi, Anna sallamay sallah liman yafara sanarwa, Yau Biyu ga wata, zulhaji, wanan bawan Allah mai suna Joseph yakarba shahada, Say wani ya rike mai hannun liman na fadin, LAILA,HA,ILLANLA MUHAMMADAN RASULLALAH,,,,, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Yan,uwa dan girman Allah ku tayi rokon Allah ya yafe min akan typing erow, da nasamu, Tun jiya duk ina cikin rudani wallahi bayan nagama na yi posting ina karanta, wa sai naga inda yanu min wai suratul Suleiman, Ina fatan dani daku Allah zai yafe muna, Ina tajiran gyara daga gare kuma tun jiyan amma sai naji shiru shiyasa nafito da kaina na nuna maku gurin, dafatan zaku yafe min,👏👏👏👏👏👏👏 Tunda ya furta wanan kalman sai ji yayi jikin shi yai mai wani irin sanyi, duk baida wani lakka, ko kuzari, Muryam liman ce tadawo dashi inda yake yana cewa, welcome to Islam Which name do u, want, in islam, neme, Joseph yakada kai yana mai cewa, a,a I will used my normal name Yusuf, Masha Allah in ji liman, You have a beautiful, name, my son , May Allah bless, u for the rest of your life,,, Daga haka aka fara shirin yi mai sadaka fisabillilah, Hannu yadaga yana mai nuna godiya da cewa ya yafe abar ma massallaci Liman yai mai alkawari da cewa duk lokacin da yake son karin haske yana iya zu don ai mai, Tafe yake a cikin motar shi yana sharara gudu zuwa gidan shi dake Girki, Yana shiga maigadi ya bude mai get,da gudu ya shige kamar wanda ake bi a baya, Baitsaya ko ina ba sai bakin fridge yadauko kwalban wani drinks mai kamshi Gaba daya ya tsotse stewvery, din ya wurgar da kwalban, Saman kujera dake cikin falo ya zauna jagab gaba daya yazube a sama, Yadafe kan shi,da hannu shi guda guda kuma ya rike gefen kujerar da yake sama kwan ce, Dad ya furta a, hankali, sai kuma sai ya furzar da yar iska daga bakin shi, Daga kwancen ya rintse idon shi sai kuma ya mike zubar yashige cikin bed room din shi, Wanka yayi yafito cikin shigar shi ta wani yadi mai dan laushi, Makulin motar shi ya dauka bai tsaya jiran komai ba ya kulle gidan, yafita, Direct wani shago dayake yawan wucewa a cikin erea, one, yanufa, Islamic center, aka rubuta bar,baro, agurin, bai tsaya jiran komai ko tambayan wani ba Inda yaga an rubuta Books Shop center, da kuma, ya shiga, Nan ya fara yar zagayawa a, hankali yana diban ire,iren littatafan da suke dashi, Idon shi yakai akan wani littafi da akai ma wani ado da green flowers,An yi,rubutu kamar haka TEACH YOUR SELVE ISLAM,,,, Yadauka sai kuma idon shi ya hango mai gurin saida cassette, nan ma yadiba yaga inda aka rubuta Suffatin Sallatin Nabiyi, Ire, iren wa yan, nan abubuwar koyar da,addini a saukake, ya saye aguri inda yabiya su kudin su ya fita, Cassette din ya fara sawa inda ya tashi daidai lokacin sallah la,asar, Yadinga yin yadda duk mai koyarwan na cikin cassette din ke yin kwatance, Har kusan dare ya kulle shi kadai a cikin gida,yana ta koyan yadda malam ke koyar da sallah a,cikin harshen hausa da turanci, Kafin wani lokaci yadan hadda,ce abin da ya sauwaka akai,, Kwanan shi biyu cikin gida bai fita ko ina ba saidai yana waya da maman choima da Ejoma, Àmma dai duk sun fahinci cewa kamar bai jin dadin jikin shi Don haka suke ta bugo mai waya, akai kai don jin ko may ke damun shi, Yadan fita waje ya sha iska don ya mike kafaer shi, Koda ya dawo sai ganin miscall, din Anty Dije yayi har biyu, Sai a,lokacin yadan ji kamar dan nishadi a ran shi, Fadar Asalamu Alaikum kalmace da tun yana yaro yahaddace ta akan shi don haka yau ma maimakon fadar hello da yasaba fada yau ga mamakin Anty Dije sai taji ya ce mata, Assalamu Alaikum warahamatul, Jin abin Anty tayi wani banbarakwai kamar bata taba jin kalman ba, Sai,ma ta rasa abinda zatace ansa, mai, dashi, Joseph yakake kwana biyu, Yaune karo na farko, da ya taba jin haushin sunan shi, Sai kuma a yanzu ya tabbatar wa kanshi da ya musulunta na tsakani da Allah, Littatafai da cassette din da yasayo na addini sun taimaka mashi so,sai gurin wayar da kai, Don ya samu haske sosai ta wanan hanyar, karatun da kallon da ya kashe kwana biyu yana koya daga malamai masu hikima,a saukake, Murmushi yaiwa anty kawai don jin Joseph din da tace mai, Anty kuna lafiya ya, jikin ki ya yara, ta amsa mai da lafiya kalau wallahi, Ya, aiki Joseph ina fatan kun rarage dai ko, sai kuma yakara ba Anty Dije mamaki da cewa wallahi Anty Dije aiki Alhamdullah, Wanan karon mamaki saida yasa tadan daga wagar dake hannun ta ta dan kalla kamar wayar ne Joseph, din, Bayan gama wayan nasu ne, mamaki duk ya cika,Anty Dije don jin sabbin kalaman da Joseph yau yake furtawa gare ta, Amma sai ta danga ta hakan da yawan zaman da yake yi cikin musullumai hausawa, Don akasarin Christian din arewa da wuya ka iya banbanta su da musullumai, Saboda akidojin su duk kusan irin na hausawa ne ita al adan hausa na isalamace, Daga haka kawai sata basar bata kawo komai aranta, ba gamay da Joseph din, Yau Monday yafito da shirin zuwa gurin aiki su inda suke son ya bunkasa masu, Mutum na farko da yafara kiran Joseph shine Alhaji, Sabo, Jin yadda Joseph yai mai sallama yasa shi saurin cewa Joseph nake magana da shi pls, Amma sai Joseph din yace, mai Yusuf dai ko,? Mamakin abin da Joseph din ya ce, Alhaji ke yi Cikin ba,a yace mai ato dayake ku a wurinku Joseph da Yusuf gudane ba Alhaji dani dakai yanzu duk guda ne ga cewa Annabi Mohammad SAW, May kake nufin fada min newai, Maganar gaskiya Alhaji, shine nayi shahada ni ma, cikin yardan ubangiji, Allah,hu, Akbar,Allahu,Akbar, yace har sau uku, yai mai fadal Alhamdullahi, Alhamdullah, Nayi maka murna dan uwa barka da shigo cikin wanan hasken, Alhaji sabo bai bata lokaci ba ya shigo Abuja gurin Yusuf, Wanan zuwan na Alhani sabo taiwa Yusuf dadi sosai don ya kai shi gurin manyan malamai na addini sunkara haska mai haske ga abubuwa, Sunyi mamakin yadda cikin dan lokaci kadan har ya haddace, wasu abubuwa masu amfani sosai daga addini, KB yadawo daga weekend din da suka tafi yi gida, don haka kai tsaye suka wuce gidan Joseph don su gana dashi akan rikicin da ya taso a ma,aikatar su jibrin Tundaga kofar da zai sadaka da cikin falon zaka ji karatun alkur,ani mai girma na tashi cikin muryan wani matashi mai zakin murya, Wani irin kallon mamaki sukai wa junan su, alokaci guda, Cak Jibrin ya tsaya don a ganin shi ba gidan shi bane suka zo wata,kila sunyi batar kai ne, KB nai yai kundun balar shiga cikin gidan kai saye, Daidai lokacin da yake ruku,u, a cikin raka,a ta biyu, Nunfashin su ne ya tsaya cak, kamar a mafarki suke ganin abin don sam basu taba tsan,manin haka ba, A,lokaci guda suka, kali junan su tare da kara matsawa kusa da inda yakai goshin shi a kasa yana sujada, Cikin mamaki suka karasa gab dashi suna mai wani irin kallo, Yusuf din ne dai yai sallamay sallah shi yana mai daga hannu yana addu,a, Har kasa inda yake zaune suka durkusa suna mai kallon shi a cikin mamaki, Yana shafawa gabadayan su suka rungumo shi zuwa jikin su Kowansu sai hawaye yake fitar wa don murna, Shiko Yusuf ya rasa ko kukan may yakeyi, daga ciki, Bayan sun samu natsuwane, suka bukaci dan, jin sanadin wanan abin, Bai boye madu sanadin shigar shi ba da dalilai dayasa har yai sha,awan shiga wanan akidar ta isalama, Shiru sukayi nadan lokaci gudu jin yadan dakatane gaba dayan su sukayi hamdallah, Jibrin yace masha Allah irin musuluntar da ake so Allah yabaka, , Badon wani bukata ba, Badon mace ba, Sanan badon yin suna ko kwadayin wani abuba, Gaskiya mun gode ma Allah daya baka dama da ikon shigowa cinkin musulunci, Allah ubangiji yabaka, ikon bauta,madhi acikin tsarkakaken zuciya, Suka amsa dafadin Ameen,gaba dayan su a lokaci guda, Jibrin ne yace Old man yasani kuwa, acewan mahaifin Yusuf din, Yusuf yadan gyara zaman shi yasa kan shi saman kujera mafi kusa da shi, Saida yanisa sanan yace nasan zamu kwasa dashi sosai Amma dai insha Allah ba matsala Allah zai kawo saukin abin, Nan dsi sukai ta hiran su ,cikinjin dadi da a,nan shuwa, Wanan zancen kamar an harba bindiga a kasuwa ne don nan a nan labari ya cika kwantagora cewa Joseph ya musulunta,,, Wasu nacewa karyane wasu, nace ai hakan zai iya yuyuwa idan sunyi la,akari da irin halinshi Abukamar yaki agidan su Joseph din don mahahaifin shi kamar mahaukaci ya koma, da yasamu labari Sam bai yarda ba kiran Joseph din yayi a waya, Mr Ema tare da sauran abokanshi Zaune ansa, waya a handfree anajira aji Joseph din abinda zai ce Kamar bazai dauki wayan ba don yasan akan,maganar da za,ai masa, Sai dai ya daure yadauka muryan dan nashi yaji ,,normal saida yadan girgizakadan, Joseph yes Dad, ya karba,mai kamar yadda yasaba ansawa, idan ya,kirashi I,want to know the true, of what, we hard here about your, Baba what's going on there, now,? Nan baban nashi ke fada mai cikin fada, cewa yarabashi yawo da yaran hausawa ga irin disgrace din da suka jamai Fada sosai baban yakamayi sukima sauran mutanen dake gurin sai cewa sukeyi, Ehhyya congurat, wooo, Na,now we hear the true, Wani iska mai zafi ya furzar tare da shafo kanshi har zuwa kasan wuyan shi, Abubuwa da dama yake sakawa aran shi gamay da maganar mahaifin nashi, Baikai ga mafita ba har tashi zuwa yin sallah, don lokaci da yaga yagabato mai, Can wani unguwa mai nisa yake zuwa yin sallah, tare da mutane, Tun lokacin da yaji cewa, yin sallah acikin jam,i yafi lada, Anty Dije ranan da maigidanta yabugo mata yana fada mata, Jin maganar tayi kamar a mafarki, alokacin,wani irin ihun murna tayi tana cewa Alhamdullaha, Alhamdullah, Allah mun gode ma, Joseph ya musulunta, maryam wace har takawo kofan falo alijacin taja tai tsaye, Musuluntafa Anty, kikace, Wanan kasurgumin Arne ai yayi nisa ko, Subbahanallah Maryam bari mana, musulmi ne fa yanzu shima Yau ba yawa kuyi hakkuri pls,👏👏👏👏👏 ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, Abu, kamar wasa magana tafara zagaye gari, cewa Joseph ya musulunta, Duk inda dan IBO yake cikin garin kwantagora da kewaye hankalin su ya tashi sosai, Don su agare su wanan mugun labari don in, su na son mutuwar su to suna son jin irin wanan labarin, Hakalin yan church din su Joseph yai matukar tashi sosai,, Meeting suka hada duk wani elder dake a church din ya halarci wanan taron, Batare da sanin Mr Ema ba wanda, sam baiyar da cewa dan shi na ita wanan abin ba, Saboda su kaf tarahin su basu da yan uwa, musulmai, balle ace danshi ya shiga islama, Sun wakilta wasu daga cikin su da zasu tafi har gurin Joseph din su samay shi face to face suji ta bakin shi, Saidai sun sha bam,bam da Joseph din don yau yabar Abuja zuwa Lagos gurin kakar shi, Sun yi kokarin bincike gurin maigadin shi amma basu gane komai ba don haka suka dawo da mamarai a ran su, Shiko Yusuf ya isa Lagos lafiya da yake tafiyan jirgine, Barci yayi sosai bayan isar shi sai musalin sha, biyu da rabi yafarka, Inda yashiga bayi yai wanka tare da dauro alwala don sallah azuhur, Key din motar shi ya dauka zuwa wani massalaci dake cikin unguwar na su, Tare da shi aka gabatar da sallah azuhur, na wanan ranan, Ibrahim wanda sai yamma yake dawo,wa daga gurin koyon computer da yake zuwa, Yadawo cike da murnan ganin Joseph a yazo gari don yasan cewa ganin shi alheri ne babba, Amma sai yaji Joseph cikkn yaren IBO yana ce mai yatashi su tafi masallaci kada su rasa jam,i, Kamar a farki yaji zancen Joseph din don bai taba tsan manin haka ba daga gare shi, Dashi akai jam,i Ibrahim wanda duk imani da,mamaki ya kashe,shi Saida yakasa tambaya don bai san ta ina zai bullo mai ba, Yusuf nagama addu,an da yadaga hannuwan shi biyu sama yana,roko tun bayan sallamay sallar ta,su, Ya,shafa a fuskan shi da gangar jikin shi baki daya, Sai a lokacin, yadan waigo inda Ibrahim yai mutuwar zaune, Hannu ya mika mai tankar yadda sunna ta tanadar wa musullumi yai wa dan uwanshi musulmi, A, lokacin ne ya mike tare da jawo hannun Ibrahim suka fito daga cikin massalacin, Cikin wani irin murya maikama da wanda kasala takama ya fara magana, Ibrahim katayani gode ma ubangiji na daya nufe ni da bani ikon gane gaskiya, Ibrahim baisan lokacin da ya,rungumay Yusuf ba zuwa jikin shi sai she,shekar kuka yafara, Bayan shi Yusuf yadan fara bubugawa shima, yana dan fidda kwalla masu zafi a idon shi, Murna yakamata kai min Ibrahim ba kuka ba a wanan lokacin, Ibrahim cikin dasashiyar murya irin ta mai kuka yace mai Dad yasani kuwa, Murmushi mai daci Yusuf, yayi wanda baikai ciki ba yace bai sani ba tukun, yai yar ajiyar zuciya, yace, Amma ,zai sani soon insha Allah, Ibrahim zan tafi da kaina in tunkari mahaifina da zance,, Duk da nasan hakan zai shafi rayuwar shi ta fan,ni daban,daban, Amma hakan ba zaisa in daina abinda nai niyad yiba don kaina, Musuluntata bata, jeka nayika bace, Ibrahim, Nayita ne don ra,ayin kaina daganin dacewar hakan, Yanzu ma na fara zurfafa acikin ta har sai ranan da naji cewa banda sauran numfashi a duniya, Don haka na shirya tunkarar duk wani kalubalin da zan samu dayin hakan Kara rungumay shi Ibrahim din yayi yana mai cewa masha Allah Allah mungode ma ubangiji Allah ka karawa Annabi daraja da daukaka, Yusuf din yakarba da fadin Ameen, tare da hannun Ibrahim don su shiga gida, Saidai yaiwa Ibrahim kashedin fada ma su mama yace sai ya fara fada wa, mahaifin shi tukun, Ibrahim yace ina mai baka goyon baya brother har zuwa lokacin da zasu gane gaskiyan ka akan hakan Ibrahim ya matse hawayen da ya cika mai ido,, yadan kalli Yusuf yace komai ukuba ko tsanani brother kada kabar addinin ka, Babana yadade yana maka fatan kasancewa a hakan saiga shi yau Allah ya karba masu addu,an su a cikin sauki, Kayi irin musuluntar da ake fatan yin shi domin Allah badon ra,ayin wani abuba, Bayan sun shiga cikin gidane maman Choima da har yanzu bata kaunar ganin Ibrahim atare da su, tai mai wani irin kallo na kaidin wa, Saboda lokacin da Yusuf baya gari sam baya shiga gidan saboda ita, A, tare sukaci abinci shida Ibrahim ranan ibrahim wanda bai damu da yadda maman Ejoma ke mai ba. Bayan kwana biyu Yusuf, Joseph, ya shirya masu tafiya gaba dayan su zuwa Niger, State, Tun safe sai zuwa magrib suka isa, cikin garin a gagauce Joseph ya aje su mama yace masu zai kai Ibrahim gida yadawo, A,lokacin Mr Ema yana kofar gidan shi kamar yadda dattijan arewa ke zama a kofar gidajen su, Gani Joseph din yasa shi jin sanyi aran shi don yasan cewa zai wanke zargin da yan church din su ke mai, A,masallavin uguwar jankidi, indagidan Abdullsamad yake nan sukayi sallah su atare da mutane Murna gurin, Abdullsamad bai ko musaltuwa, Yai ma Yusuf nasiha akan yadda zai tunkari mahaifin shi akan zancen, Da murna sosai mahaifin nashi tare da yan uwan shi suka tare shi, Sai murna sukeyi da zuwan shi fiye da yadda ma kullun da yake zuwa,sukeyi Sun ci abinci kamar yadda aka saba sun dan fara,hira can, mahaifin shi ya jefo zancen, Musuluntar da ake cewa yayi a,gari inda har mutanen, su sunfara yimai wani kallo, Joseph yadan sunkuyar da kan shi kasa ahankali, sai yadago sukayi ido biyu da mahaifin nashi, Yusuf yace a hankali is true Dad iam now Muslim, Cike da mamaki mahsifin nashi da mama suna kojarin hada baki gurin tambayan, abinda su,ka ji kamar yace, Yusuf yadan yi shiru can yace Iam Muslim now, Cikin wani irin fushi mahaifin shi ke magana acikin harshen IBO Mafarki kakeyi Joseph ko ko wasa,indan har haka kai ma,za kadaina don ban son irin,hakan, Baba bawasa acikin zance na sam, gaskiya nafada bana cikin addinin ku yanzu Wani irin ihu Mama choima ta sake wanda yai kama da ihun mutuwa, Mr Ema wanda ya suma azaune bai masan ida yake ba alokacin, sai Yusuf din ne ya dan kula, Yai kanshi ya na girgizawa a hankali yana mai kiran sunar shi, zuba mai ruwan sanyi yayi, yadan farfado, Duk da acikin dare ne suke wanan abin bai hana wasu makwabta jin hayaniyar su ba, Abokin Mr Ema ne yashigo lokacin don jin cewa Joseph ya shigo, gari, saboda shim a matse yake da yaji gaskiya don yai wa mutanen su, sheri, John yayi matukar kidimay wa don ganin irin yadda abokin shi yake zaune jagwab, sai wani abu yakeyi kamar kaza tasha ruwa, Mama Choima wace tsananin rudewa yasa ta faduwa kasa tana ta rusa ihu, da shure shure, Tana ta zabga gwalanci cikin yaren su,na IBO duk a kidime take wanan sanbatun, Yusuf wanda ahalin yan zu ya mike da ga tsugunin da yai a gaban mahaifin shi, Y Wanda shi da kanshi Mr Eman bayan yafarfado yai wa Yusuf din hannu alamar yajaye daga gurin shi Ke nan baya son ganin shi agaban shi Yusuf wanda zuciyar shi tariga ta keykeshi bai jin ashhh, Ya mike tsaye batare daya tsaya ko ban hakkuri ba, yakama hanyar zuwa dakin shi, Hey stop, there mr man, don't enter my house, pls, Yusuf yai tsaye kamar mai tunane nadan wani lokaci sai kuma ya juya kawai yai hanyar fita waje, Cikin wani karaji maman choima, ta mike tsaye ta je tasha gaban shi tana mai tare shi da hannu, Kada katafi my son idan katafi ,zasu kara rudin ka su cutar dakai da addinin su, Mahaifin shi yace mata tabar shi ya tafi tunda yanaganin kamar cewa suna son shine don Allah badon kudin shi suke son suyi amfani da shi ba, Yusuf Joseph yadan dago kai yakali mahaifin kamar wanda zaiyi magana sai kuma ya fasa, Ganin irin kukan da mama keyi yasa shi juyawa zuwa vikin gidan nasu, Mr Ema wanda baikara yunkurin korar dan nashi ba wandda a shirye yake, da yabar gidan, Tun shigan shi dakin shi sai yaji duk tausayin mahaifin nashi da kankashi, Harma da yan uwanshi da,ke tafaman kuka cikin tashin hankali, Amma saidai ina yai nisa ko acikin Isalama, baya jin kira, Zima yana mazu fatan Allah yas su gane gaskiya sudawo hanyan gaskiya, Sai cikin dare sosai barci yadauke shi, ko shi sama sama, Don tabatar wa cewa yana cikin musulunci da shi aka tafi, sallah asuba wanda yai daidai da yadawo daga masallaci sukayi kicibis da maman chiloima Wace tafito tin cikin dare takasa barci, suna yin ido biyu dashi sai ta hau wani irn gumza da ihu cikin kuka tana magana kamar mara hankali, Kai kawai yakada yana mai murmushi abinda yaga tanayi wanda shi sam tama fara bashi dariya a,lokacin Acikin takon shi maikama da kasaita, yafito, Bakajin komai mai sai karan takon takalmin shi daya karade falon Zazzaune suke kowanin su ya kurawa abincin dake saman table din ido, Wanda sam yau duk kyau abincin bai,basu sha,awa, Fita yai niyar yi a,lokacin, batare da yako kalli inda suke zaune ba, Mama ce tai karfin halin yimasa magana da cewa son kazo kaci abinci kafin kafita, Mahaifin shi wanda yai kicimkicim da fuska, ya zauna ya hade hanna yen shi guri guda yatokare habar shi da su, Yusuf wanda alokacin yafara kyamar abincin su don ganin irin dan bujen dake ajikin su ga,wani gashi doki da suka jibga,akan su, Inda take ya,dan taka cikin tako irin nashi ya dan rungumota tabaya yana cewa yanzu zai dawo ai bazai dade ba ai, Cikin fushi Mr Ema yace ya sake ta tunda baidamu da damur su ba, Sai yanzu yagane komay yasa tun farko ya ke bin diyan hausawa da musulmai Mr Ema cikin daga murya yake fada da Yusuf yana cewa, Tunda naga mahaifiyar ka ta haife ka lokacin watan da musulmai suke azumi, Har suna zo muna murna wai na haifi, yaron lokaci mai kyau,,,, Sai yadukar dakai kasa cikin bacin rai yakasa cigaba da bayanin dayakeyi, A wanan lokacin members na church din su sun kai su goma sha, suka shigo, Daya bayan daya Yusuf yakalle su basai an fada mai ba yasan komay ke tafe dasu daga shi har mahaifin nashi, Kallo guda Yusuf yai masu ya kauda kai don dai kawai bazai ita masu rashin kunya bane da halin shi da yau yai masu, Wani dan tsamurare daga vikin su maikamar shagada Yace Joseph what's going on pls,? A hakali yadago kai da idon shi da yai jawur yace, Iam now Yusuf not Joseph Mamaki karara a fuskan su wanan ya kalli wanan wancan ya kalli wancan, Maman Choimal wace sai hawaye takeyi cikin tashin hankali, ta na dan kada kafar ta cikin fitina, Wani daga cikin mutanen wanda bai,karkare kai sauran shekaru ba ya ce Umm,ba, Look mr let's have a serious talk pls, Yafara magana acikin yaren su, kamar hakan ga, Joseph may yasa kai wanan clash, din pls, Mace, dukiya, ko suna, friendship? Ido Yusuf ya kura mai don shi dai ma tausayi yake bashi shi mai maganar alokacin, Don haka murmushin takaici yai mashi yana mai sauraren shi a natse, Mai maganar yaci gaba da cewa idan har saboda soyayya ka koma ai muma muna da mata madu kyau daga cikin mu, Idan kuma dukiya kake bukatan kari kafadi daga milliyan zuwa sama zamu hada maka Haka kuma idan suna kake,,,, Da hannu Yusuf ya dakatar dashi alamar ya isa hakanan Baison karasa sauran shirmayn fon jin maganar yakeyi kamar may tatsuniya, Sosai yabude idon shi yau gare su yafara da cewa, Kudi mace, suna duk ni Alhamdullah, yana,mai pointing din kan shi, Ra,ayi ne kawai bawai don wani abuba nashiga nadaiyi nazari naga cewa itace hanya mafificiya, dazata fissheni, arayuwata, Daga haka yamike yana mai hada hannayen shi gurin daya yana cewa da kaga yai pls kada wanda ya kara maganarr, Daga haka yasa kai fuu, yafita ya gidan batarecda yai ma kowa sallama ba, ZEEE MAKAWA,,,,, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,, Bayan fitar shi daga falon Mr Ema wanda ke zaune cikin tashin hankali tunfarko yai wani irin dan ihu, sai kawai fashe da wani irin kuka mai tsuma rayuwa, duk wanda ya saurara, Cikin sauri ,wa"yan da ke kusa dashi abokan shi suka dan riko shi cikin kulawa, Mamsn Choima wace sai ye, Jesus come help me wooo, Samuel dasu Ruth sai wani irin ihu sukeyi suna cewa please brother don't do that for us woo, Gida ya rude da wani iri sabon kuwa kamar an masu mutuwa, Har masu zuwa tambayar wasun su suka fara,ihu da kuka na bidan taimako, daga Jesus, Shiko Yusuf yana barin gidan su gidan su Jibrin ya fara zuwa Inda yasamu mahaifin shi ya sheda mai da kanshi saboda girmamawa, Don yanzu yasan cewa sunyi mashi halarci sosai don basu kyamace shi ba alokacin da yake abin kyama agare su, Baba yaji dadi kwarai xa wanan karamcin da Yusuf, yai masa, don jin dadi har da hawaye yayi don farinciki, Yana murna adduan shi takarbu ke nan don a saudiya yai ta mai addu,an Allah ya nufe shi da komawa cikin islama , Saboda kyawawan halaiyan shi da yake yi tankar ba dan, Ahalal,Kittabu ba, Nan Baba ya kara lurar dashi kyawawan hanyoyi acikin al,umma , Daga gidan mahaifan jibrin bai tsaya ko ina ba sai gidan Anty Dije ya nufa, sai dai kafin ya isa can saida ya tsaya yai masu tsaraba mai yawa, tukun, kamar yadda yasa ba, Maryam duk kwanakin nan bata jin dadin jikin ta,tana fama da mura, har takai bata je makaranta ba yau, alhamis, A,A daga school ya zo diba lafiyar ta don ya san cewa maryam batason magani ko allura Shine ya sayo mata wasu maganin da ke maganin murah, Tsaye suke a kofar gidan su, A,A yana rike da marfin kofar motar shi kafar shi guda yana ta cikin mota, Maryam wace ke tsaye,sanyi da farin hijabin ta, Idonta da suka dan yi ja saboda murah datake fama dashi, suna dan lunshe, Suna facing din juna ita da A,A din sai dai dagani ita Maryam din tana nuna yar kunya take ji, Tun,daga nesa ya hango su a tsaye ya kuma gane cewa itace a gurin tare da A,A, Saboda yasan cewa suna tare, dashi, dadewa sai dai shi sam guy din bai kwanta mashi ba arai, Don siffan wayewar shi tayi yawa, sosai yafi karfin wayewar yarinyar, aganin shi, Alokacin da ya tsayar da motar shi dan nisa kadan da ga inda suke tsaye Bai,fito ba amma dai kamshin shi,turaren shi ya isar da sakon cewa shine a,gurin Yadan jima zaune acikin motar shi yana wani abinda sudake ta waje ba su sani ba saidai rabin hankalin shi A,A din yana gurin Yusuf din, A,A a zuciyar shi mamakin irin yadda Joseph karamin matashi dashi yake shiga irin wa yan nan motocin haka masu mugun tsada, Maryam ce ta,katse mai tunanen shi da cewa, Kuji wanan yazo ke nan zai damu mutane kwana biyu yahana mu hutu, Haba dai ai yanzu kudashi kun zama daya don irin shakuwar shi da gidan nan yai nisa, Kam wallahi kan bamu zama daya ba taya zaka hada mu da arne wanda bai sallah, Kawai dai yana zuwa ne don yaran nan sune abokan hiran shi, Kina da sauran fahinta maryam ai zuwa yake yi kawai don gari su dauka cewa yana hurda da musulmai bawai yana kin su ba, Amma wanan ai irin mishon din,nan ne bat da musulmi, Kagan shi kamar na Allah amma cikin zuciyar shi baya kaunar musulmi ko kadan, A daidai wanan lokacin Yusuf yafito daga cikin motar, shi , direct inda A,A ya ke tsaye ya nufa yana mai mika mai hannu yana cewa Assalamu, Alaikum, Gabadayan su saida sukaji wani irin don jin furucin shi na yau, Saboda sam ba su sancewa Christian suna sallama irin ta muslumai ba, Saida maryam tadan nisa tukun tare da jan dogon numfashi,, Cikin mutunci Yusuf yagaida A,A, wanda ke da sauran mama a makale a fuskan shi, San nan Yusuf yadan waigo inda maryam take tsaye rakube a jikin bango, A,hankali ta furta sannu da zuwa, saboda wani kwarji da taga yai mata a ido, Yusuf din yakalle ta suka hada ido sai, tai saurin sunkuyar da kai kasa, Wani irin juyowa AA yayi wanda bai, masan lokacin da yai hakan ba da wani irin mamaki ya kara baiyyana a fuskan shi, Daga Yusuf har Maryam wace kanta na ,a,duke, lokacin ba wanda yasan yana yi, Ciki ya shiga direct, saidai yadan tsaya ta kofa kadan ya kwada sallama, Sabanin da dayake shiga sai yakai ciki yai sallama, Assalam wanda sun dawo daga school ke nan,yana kwance falo yana home,work, Zubur ya mike saboda fahintar muryan Yusuf da yayi, ba yau ba, duk inda yaji muryan shi zai sheda shi, Da gudu ya sheko ya rungumay shi, don farin ciki Shima din rugumay yaron yayi yana mai jin dadin ganin shi Anty ta fito da fara,ar ta,cikin ta wanda har ya fito, Anty Dije tace mun yi fushi da mutanen Abuja ne ko Lagos, Yai yar murmushi ya shafa guskan shi sai kuma ya kama kan Assalam zuwa kofar falo, Inda Anty Dije ta bude mai don ya shigo, gaskiya ba laifi hakan yasa yake kara son gidan Anty Dije don tsabatan ta,, Komai na gidan,ta tsab zaka gan shi bakamar na sauran gidaje ba, Yusuf da murmushi a fuskan shi yazauna yana mai cewa Anty Dije mun samay ku lafiya, Nan suka fara hiran zancen maciji da yasa su agaba a ma,aikatar da sukeyi, Nan dai yafara,ba ta labarin yadda abin yafaru, atakaice, inda Joseph, din yace, gaskiya sun bashi tausayi dayasan suna gurin zai iya sayen gurin yabarshi don su kawai, Amma saida aka kore su ne yaga yadda suke da yawa kamar tashin hankali, Maryam wace tunda ta tunkaro shiga gida take jin muryan Yusuf Cike da jin haushin yadda Anty ke wani nan,nan dashi, take ji, Da sallama tashigo amma kanta yana gefe cike dajin, haushi, lokacin, Kamar mai rada yace, don Allah in,ba takura,ki karbi wanan key din ki sa,a kwasowa yara, tsarabar su a bayan mota, Ganin yadda ta tsaya sanin bata jin dadin jikin ta, Tace wa yar uwar ta,ta, zaki iya kuwa Maryam, ko kuma kisa wasu yara su kwaso sai a sallamay su, Sautin murmushin shi taji yana cewa anty aiba wani abu mzi yawa bane bari kawai in,fita in,kwaso, Dama don naga wanan guy din a kofane shiyasa ban shigo dasu ba,, Key din da ya mika mata ta duka daniyar karba batare da tai wani magana ba, Cikin rashin , shikuma ya yunkura yatashi,don ya,tafi ya kwaso kayan don ganin ledar magani da yai a,,hannunta, Fuskanta da goshin shi suka dan gwauri juna, har sai da tasa yar kara, tadago ta, dube shi amma sai taga idinshi kamar na mai jin barci, Da sauri ta kawar da kanta daga kallon shi, tana mai dagawa, Muryan ta narawa, tace mai sorry pls, Key din dabata daukaba ke nan ta nufi hanyar dakin ta, Shiko Yusuf kamar bashi ba, ya mike a hankali rike da hannun Assalam, suka fita daga falon, Kayan da yace bayawa su maryam ke jin anata jibgewa a falon, a ranta tace shine wai bayawa, Takuma kara cewa wai shi wani irin mutum ne wanda baya jin zafin kashe kudi, ne haja Dama ace shi musilmi ne da ya more rayuwar shi wallahi, Muryan shi taji yana cewa anty Dije kiyi hakkuri Anty, Kafin ya karas fadar abin da zaice sai sallamar wani kanin mijin Anty Dije ya katse mai maganar, Nan ya fara mai hira irin ta maula suna ta zance irin yanayin da kasa ke ciki a lokacin, Har wani Ladani mai zakin murya a wani masallaci dake makwabtaka da unguwar su, Yana kiran sallah azuhur, Agigon dake daure a hannu shi ya diba sai ya mike zubar yana mai kokarin sance agogon dake a hannun nashi, Inda Assalam yake ya dan kalla yace mai, dauko muna buta, friend Da gudu yaron yatafi,batare da wani mamare ba, Anty Dije wace a lokacintake duke tana kaida kayan da yara suka zube mata akofar falo, Tai saurin dagowa daga duken da take tadan kalli Joseph wanda ke kojarin tankwafe hannun rigar shi da kyau, Ba shiri yafara gagauta alwalar shi, batare da yai wa kowa magana ba har yakare, Duk,kan su suna tsaye soro, suna ganin ikon Allah, Anty Dije wace cikin mamaki take kallonshi har zuwa yanzu da yake kokarin mikewa ya rikowa Assalam hannu, Yana yar murmushi yace barin dawo anty kawai saikiji karin bayani, Tun zaman ta da Yusuf sai yau zatace taga fararen hakoran shi a waje, Nan yabarta cikin mamaki yai saurin wucewa massalaci, abin shi, Wani irin dariya da ihun jin dadi Anty Dije tasa a lokaci guda Wanda hakan yasa maryam daje kwance daki tana shirin barci dirowa daga saman gado tayo waje don ga ni komay ke faruwa da yar uwar na ta, Lafiya Anty, maryam ke tambaya cikin nuna zakuwar ta, da son ji komay yasamu haka na farin ciki, Maryam Joseph ya musulunta fa da,gaske maryam wace ke tsaye daga nesa kadan da yar nata, Ai, tsale guda tayi sai gata agaban anry Dije tace kai,fa Anty, Keda ke daki dani da jamil mukaga mamaki yanzu ai, Don kinga inda yai alwala yanzu yafita, zuwa sallah, Allahu Akbar,Allahu,Akbar maryam ta iya furtawa kai don komai ma ya bace mata, alokacin, Nan suka shiga murna tankar wani dan uwan su ne na jini yasamu wani alheri, Yakai wani lokaci kafin ya dawo dga massalacin inda yasamu har Anty ta idar da sallah tana zaune tana addu,a, Saida ta shafa ta waigo inda yake taimai murmushi tace ashe labarin da muke ji da gaskiya ne, Yace Anty Allah ya nufa kuma likaci yayi, nan yafara ba Anty labarin tun yadda ya kai kanshi massallaci gurin, liman har zuwa yadda sukayi da mahaifin shi, Ysu din yafada matacewa shi musuluntar shi ba gudu baja da baya Don Allah yayi abinshi sun dauki lokaci tare da Anty yana bata labarai masu ban tausayi gamay da irin halin rayuwar da ya shiga, da kuma wasu ire, iren yan yaren su da indan suka musulunta irin wahalar da suke sha, don rashi kula daga yan uwan, jinsin isalama, Cikin canza fuska wace ta sauya zuwa ta ban tsusayi, yace ma Anty Dije, Matsalata guda yanzu yadda mahaifina zai shiga wani hali, don nasan zai sha wuya gurin yan uwan shi tare da members na su, Amma idan nadaure nasan cewa komai zai wuce insha Allah Tare da Assalam suka fita zuwa gidan Abdullsamad, Nan ya kwashe duk yadda sukayi da mahaifin shi yafada mai, Dan dattijon yana mai girgiza kai yace sai kayi a,hankali yanzu don duk wani hanya nasamun ka zasuyi kokari suga cewa sun, kawo ma farmaki, Zasu iya bin duk wani hanya don su,ga cewa sun saka acikin wani hali, Yusuf wanda ke zaune yana sauraren dattijon yai yar murmushi mai nuna takaici aciki Dattijon yace yes mahaifinka nasan halin shi, sosai Yusuf zai kawo ma attacks sosai, Don ban manta irin abinda yai min ba , alokacin da na shahada kamar ka, Nan yabawa Yusuf labarin duk yadda Mr Ema yaita sa a,na,kaimai attacks, Sam yusuf baiji dadin wanan labarin ba don a yadda yasan mahaifan nashi atare bai zata, zai iyasa ai ma haka ba, , ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Barkan da jumma,a yan ,uwa Allah ubangiji yasada mu da alherin dake cikin wanan ranar mai albarka,👏👏👏 Maganar da Abdulsamad ya fadawa Yusuf gamay da mahaifin shi ya tsaya mai arai, sosai, Don haka yasan cewa ko shi bai tsira ba ke nan don mahaifin nashi zai iya yin fiye da haka akan church din nasu, Don haka ya sa a,zuciyar shi cewa, dole ya dauki duk wani mataki wanda yasan cewa ,za,a iya kawo mai hari akai, Washe gari ya kasance ranar jumma,a ce, don haka tunda zai fito ya fito da kayan da zai shirya kanshi a ciki Don barci kawai yakaishi gidan su cikin dare sai dai ya kula da cewa kamar an,masa bincike a dakin, Murmushi yake yayi shi kadai a cikin dakin, don haka duk wani abin da yake bukata ya hada su guri guda, Tunda safe da zai fita yakwasa sai gidan, Ànty shi Dije itace yakai wa ajiyar kayan shi masu muhinmanci, dake gidan nasu, Maryam wace ke zaune a lokacin gaban mirrow tana make-up, Taji muryan shi ya na ta kwada sallama akofar shigowa gidan , Haka kawai taji zuciyar ta ya tsinke mata, kamar mai tsoro, Zubur ta dan yi ta mike a gaban mirrow saboda ta sheda ko muryan waye, ke sallamar, Saidai, yau ta tsinci kanta da dan jin nauyin ansa mai sallamar tashi, Saboda irin yadda tai hating din shi a matsayin shi na Christian a da, A,ciki ciki ta ansa mai sallamar tashi, kamar wace ke rowar magana, Dankwalin da tafara daurawa rike a hannun ta tadan leko tawaje don tabashi izinin shigowa ciki, Saboda Anty Dije tana bayi gurin wanka alokacin, Ido biyu sukayi dashi, yana saye da wata riga mai hannu iya damtsen hannu, sai wani dan ado da akaiwa hannun rigar kamar kwalar riga ta wuya, Shima wuyar rigan irin hannun rigar ce akai yi ta, Sannu da zuwa ta furta acikin muryan ta makama da ta rowa kullun, Sai kuma can tace tadan shiga wanka yanzu zata fito Abinda kawai ta iya fada ke nan a darare, kamar mai jin tsoro,, Fuskan shi a natse kamar kulun yace ba matsala ga wanan pls ki bata ta aje min zan je in dawo, Sigar da yake maganar shiya sata dan dukar dakai don komai nashi a kasaice yakeyin shi, A, hankali yatako har, gaban,ta ya mika mata jarka Wace batasan ko tamaye ba,ita,dai ta karbane kawai, Har yabar gidan tana tsaye a inda ya barta rike da jarkar da ya miko mata, Karar rufe kofar shiga gidan ce tasa, Da sauri ta juya zuwa ciki, sai yanzu ma taji haushin fitar da tayi da tasani ma kawai ta amsa mai ata cikin daki, Turus tayi a folon ganin, Ànty Dije zaune tana shiri abinta acikin natsuwa, Anty ce tace tomay zance tunda kin ce masa na shiga wanka ko, Inda take ta nufa da jakar ta aje saman wani kujera tafita batare da tai wani magana ba, Yusuf kuwa yana barin gidan su Anty, kasuwa yatafi Abinda yaksi shi kawai shine yasamu shago babba mai kyau yasaya, Allah yabashi sa,a yasamu shago irin wanda yake so, Ba bata lokaci akai komai yasa hannu ya biya, Kafin tabar gurin har cikin IBO dake layin sun sheda wa mahaifin shi cew gashi a kasuwa yana diban shago, Ganin lokacin sallah jumma,a yana gabatowa shiyasa yai haramar komawa, gidan su Anty Tafe yake yana shawara a,ranshi cewa gobe zai tafi gurin mahaifinshi,yasanar dashi, Cewa ya sai ma Abdulsamad shago saboda Allah da Annabi Saboda duk irin halin kuncin da ya jefa Abdulsamad din saboda akidar addini yasani, Don haka zai fara sanar dshi cewa sun san mugun halinshi akan wanda duk ya canza addini daga cikin su, Yasan idan har yafada mai garan dagaran zai samu saukin duk wani kulli da zasuyi mai, Yana cikin shawarar ne azuciyar shi har ya kawo kofar gidan Anty Dije, Wanda kawo,war yai dai,dai da lokacin da A,A shima yake kokarin aje motar shi don sauke maryam, Da ya dauko daga school, don yau jumma,a bata wani dadewa, a school din Sun,na zaune acikin mota, suna dan taba hira saidai kafarta guda yana a tawaje da sauran jikinta, Hikimar yin haka gareta shine kare zargin yan unguwa masu sa ido a masu zama da maza cikin mota suna masu suna, Kallo guda yai masu ya,kauda kai, gefe, guda batare da yakara ba, Don yarasa komay yasa sam baya son yagan su atare da wanan guy din, Yasamu Anty ta aje mai abin karyawa a falon ta bayan sun gaisa ta gabatar mai da abin kari, kumallo, Sai yaji wani irin kara girmamata yashige shi shiyasa yake son al,amarin ta, don tana saurin fahintar shi, Muryan ta yaji tana cewa, tasan cewa baici komaiba har yazu saidai tana gani abincin yai sanyi ko zuwa yanzu, Ya zauna ke nan da niyar fara ci maryan tashigo gida cikin takon takalmanta da ke fidda sauti, Tundaga kofa tai arba dashi cikin sauri takawar da kanta gare ahi adaidai, lokacin da yake kokatin zuba ruwan zafi a cup Duk da takwaso nata kalar yunwa baisa ta tsaya don ta,karya ba sai shigewar ta tayi kawai aciki Anty Dije ce tasa mata kira don tasan cewa itama bataci komai ba tau tabar gidan Alokacin maryam harta cire hijab dinta daga ita sai wani English wear buje da riga masu kamar son shagewa a jikin mutum, Sam har ta manta da cewa akwai mutun a gidan nasu, Don haka bata tsaya sa wani hijab ba kawai falon ta fado Duk yadda taso ta tare jikinta hakan bai yi ba saboda kayan sunyi mata masifar kyau, Shiko Yusuf kallo daya yai mata yakauda, kan shi gare ta Abinda baka ra,ayi ko ya yake bazaka sahi arayuwa,ba, Tunda bawai wani abune atsakanin su ba baiko dauki ganin ta haka dayayi dawata manufa ba, shi, Itako sai kokarin kamay,kamay takeyi, don kada yakalli surar jikin ta, Wayar shi ce ta sa kara alamar kira,, Aisha ya furta a hankali, sai kuma alamar yar murshi dayayi alokacin Hakan ya,tabbatar masu gabadayan su cewa da Aisha yake wayar, Maryam ta juya bayan tace wa Anty ba ta jin yunwa,, Tashige abinta batare da tatsaya jin kwam ba awayar da yake yi, Bai wani dade ba yai ma anty dije sallama yace zai je ya shirya yazo tadauki Assalam su tafi, massalaci, Shiga,sosai yayi na Muslims farar shadda ce dinkin ta,zarce Wani hula yasa mai ruwan, siminti, sai takalma shige hular kan shi, Kamshi agurin shi ba,a maganar, yana rike da wani bakin tasbaha kiran China, Bai wani tsayawa ba don yana sauri, luckily ya samu an shirya Assalam ko, suka tafi, Maryam wace ke tsaye daidai kofa ta sauke wani sanyayar ajiyar zuciya, Ta waiga ida anty take tace cikin tabe baki yayi sa,a gaskiya da Allah yanufe shi yakarba kira, Murmushi Anty Dije taimata tace abin ai daga Allah ne maryam, Shiyasa mutum idan kasan farkon shi aibakasan karshen shi ba, Sun isa massalaci anata zuba sahun a ko wani bangare, Tareda Abdusamad sai jibrin da KB da suka uso da ranan nan, sai Ibrahim da yake acikin su, Ido akan su caaaa wasu duk da a cikin massalacine harda leke sukeyi idan an nuna masu shi, Hakan sai bai wa Yusuf dadi ba saboda irin yadda ake mai babu ko boyo, aciki, A, cikin zuciyar shi yace, to komay kuma ya yi da ake mai haka, Don shi ai tsan mani yayi za,ai farin ciki da kasancewar shi acikin wanan massallacin mai,albarka wanda yatara dinbi musulmai, Duk da ana sallah amma wasu yan gulma idon su yana kan shi don suga yaya zaigi sallah shi, Bayan an sallamay sai kawai sukaji ana, musuluntar nashi a she mahaifin jibrin ne yabada wanan sanar wan Aiko mutane sai nunafarin cikin su sukeyi don dama andade ana rade radi, Da kyat suka samu su kabar harabar massalacin don yawan jama,a masuyi mashi barka, Labari ya iske Mr Ema cewa ga abinda yafaru a massalaci wanda wasu musulman mune suka kwarmatawa wasu daga cikin Ibon garin, Mr Ema shida yan tawagar church har mada na wasu churches din sukayo kwamiti zuwa gidan Sarkin Sudan, cikin fada, Don su azaton su, zadu ita shawo kanshi, jira sukeyi su gama aiwatar da shirin su, Sai gashi anyi anoucement, a massalacin jumma,a cewa ya musulun ta, Sarki yasa aka tare su, cikin dan mutunci, Inda yasa sugabatar da abinda,ke tafe dasu Rankashidade, muna karan wasu yaran musullumine gurinka cewa su ja yalon mu zuwa ciciin Muslims, Batare da bakin mahaifinci ba, Eheh, shine munzo mu fada ma,ka, shewa, muna son abamu yalonamu, afido dashi daga shikin isalama,wanda ya ciga,,, Bayan mai martaba yagama jin korafin su ne, yadan magana da galadima,da waziri, Galadima ya ari bakin mai sudan yai masu bayani kamar haka, Muna son kuzo da yaron na ku nan don muji ta bakin shi, sanan, a kira wa,yanda suka maidashi ciki, Fita sukayi daga wajen fadar maimartaba Sarki Sudan Suna ta kus,kus ta yadda zasuyi su kawo Joseph gurin sarki, Shi Mr Ema dakanshi, ya kira Joseph da wayar shi, kira daya ana biyu ya dauka, Joseph come nd meet me in mai Sudan palace now,now Yusuf wanda ke tare dasu KB suna wani estimate, din kaya, Abin yabashi mamaki ya kalli su KB yace masu cikin bacin rai wai Dad dina ne fadar mai sudan, Duk kan su cikin mamaki, sukace gurin mai Sudan fa,? Sun so su bi shi sutafi tare amma yusuf din yace su bari kawai zai iya zuwa, Mr, Ema tare dasu Ekewa, da su Barnabas Mr Ema wanda ke zaune cikin damuwa ya saye da wani rigar yadi mai hoton giwa, dajan colur, sai wani jar hula dayasa akan shi, Yana rike da sanda a hannun shi,,maikama da kan gunki Kallo guda zakai ai kane cewa yau rayuwar shi ba tada dadi sam, Su na ganin shi sukayo kanshi caaa kamar zasu ciye shi danye acikin yare suke magana suna cemai, ya taimaki rayuwar shi kada ya bari wasu su rude shi, Kowa daga cikin su da abinda yake fadi, don dai kawai ya amsa cewa bai musulunta ba, Zazaune suke gaba dayan su a gaban,mai sudan, Inda mai Sudan yasa akara fadar abin da sukazo dashi Yusuf na sauraren yai shiru saboda ladabi har lokacin da aka gama bayani akan komai, Maimartaba ya kurawa Yusuf ido har nawani dan lokaci, Sai yagano cewa Yusuf wayayye ne bazai ce Yes ba, yace No ba kuma Don haka sai sarki yace mai samari kaji bayanin da iyayyen ka sukazo, dashi, Zaman shi ya gyara cikin ladabi yakalli inda maimartaba yake, yace, Assalamu Alaikum warahamatullah, Sauran musulamai dake gurin suka karba mai kamar yafda sharia ta ce ayi, Suko gaba dayan su suna jin wanan kalaman da ya fara magana da ita, suka dau da cewa Emba, Juses crisis, Oluwa, inji wani pastor yan olumba,olumba, yace cikin kada kai alamar takaici wai,, Yusuf yace a gaskiya babu gaskita daga cikin zancen su, Saboda ni yanzu nakai munzalin da ,zan daukar wa kaina duk abinda nake ra,ayi, Heh Joseph come to your sense pls ? Don't deceive your self Magan ganu iri iri suka dan fara cikin, jin haushi da takai ci, Nan da na fadawa suka daka masu tsawa dole suka natsu sukayi shiru Yusuf yaci gaba dacewa, Nazama musulmine ba tare da sda shawaran kowa ba,, Ra,ayinane kawai yabani shawar gane hanya afificiya ta isalama, Kai Na, lie, woo, Wani bafade dake, kusa da mai maganar ya watsamai bulala tauuu, Yace mai cikin daka tsawa behavi your self Ganin haka yasa du natsuwa dole zuciyar su na suya Yusuf yaci gaba da cewa, banzama musulumi ba saida nasamu kwararar hujjoji daga Alkur,ani maigirma, Eyy,Eyyyy, he's finish wooo, Abinda sukace gabadaya kusan lokaci guda ke nan, Watau, Joseph ysi nisa har da Alkur,ani ya,yarda dashi,, Yusuf yace saida na hada duk wani hujja wanda zanyi depending a kai sanan nida kaina nakai kaina wurin limamin central mosque na Abuja ya musuluntar da ni, Saboda haka duk wani wanda ke zargin cewa wani ne yajani zuwa cikin islama ba gaskiya bane, Ni YUSUF ban musulunta akan abin duniya ba ko mace ko aboki, Na musuluntane saboda Alkur,ani maigirma, Sai duk wanda ke cikin fadar musulumi suka dauka gaba daya dafadin Allahu Akbar, Yace nakai lokacin da zan zabawa kaina abinda nake so daga addini, sana,a da kuma iyali, Cheer, God wooo, He, don go far, A nan maimartaba yai masu warning akan cewa duk wani wanda ke son kawo mai fitina ko tashin hankali acikin kasa ashirye yake da yadauki mataki akan mai shi tunda har wanda suke magana yace ra,ayin shine shiga addinin da yakeso don yakai shekara talatin, yanzu, Kuka sosai Mr Ema yadinga yi acikin fadar mai martaba yana fadin cewa a taimake shi amayar mai da danshi cikin Christianity, Amma ba wanda ya bashi goyon baya haka suka tallabe shi zuwa bakin motar dasukazo dashi yana kuka, wi,wi, Yana kiranan sunan joseph yana zuba gwalancin su, Shiko yusuf dama yarigasu barin gurin don haka gidan Anty Dije yakoma, Saboda yadan samu relief of mind, din shi sai,dai kana ganin yadda idon shi ya rine kamar garwashi zaka gane cewa, yana cikin tashin hankali, Yadan dade yana waya da Alhaji sabo inda yake fada mai abinda yafaru dashi yau da mahaifin shi, Maryam wace ke cikin bayi a lokacin tana jin abinda yake fadi har zuwa lokacin da yashigo ciki da rinanun idon shi, Falo yazauna jagab saman kujera two siter dake cikin falo, Maryam wace kafin yashigo,,tafito ko daga bayin Tana cikin shigar atamfa, buje da riga masu ruwan multi, colour, Dinkin yai mugun karban jikin ta kayan da tasane tai adon jin ma,a dasu, da rana, Taso taje ziyara gidan su safiya amma sai taga yau Anty bata jin dadin jikin ta sai tafasa shine tashiga bayi ta gyara jikinta don tana fashin sallah, Acan ne taji muryan Yusuf din yana waya dawani yana fada mai irin yadda yaji gamay da mahaifin shi, Wani irin tausayin sa taji don tasan da zafi ace mahaifinka na kuka akan ka, Inbadon addinin gaskiyabace kamar yadda Yusuf din yace da sai ya fasa yakoma gurin mahaifin shi To amma ba,zai iyaba sam ya shiga isalama kenan har mutuwar shi acewar, Bashiga bafita shiga sojan badakkare, Tana bude labulen dakun tafitowa suka hada ido, ya sakar mata rinanun idanun shi da suka kada sukai ja , Kan ta, takawar gefe cike da jin tausayin shi alokacin, Direct gurin fridge tanufa tabude tadauko kwalin madarar youghot mai sanyi mai hoton bafillata, na company Mrs Ghali, youghot, Ta hado da cup din glass bata tsaya ba sai,gurin shi direct, Ta, dan rage tsawonta ta fara zuba wa acikin cup din a hankali, Sai a likacin yuduf ya bude idon shi dasuke lumshe yasauke su akanta, Ta mika masa youghot din a hankali, batare da ce mata kala ba yakarba , Yakafa kai a hankali yana lumshe ido don sanyi da gardin youghot din, Saida ya shanye glass guda a hankali ya cire cup din abakin shi murya kamar mai rada yace nagode Maryam,,, Maryam ta mike daniyar barin gurin don jin ajiyar zuciyar da yayi, Yace may ye sunan wanan madarar, A, hankali tace Mrs Ghali, youghot, Masha Allah yana da kyau,,, ZEEEE MAKAWA [3/11, 10:18 AM] ‪+234 808 968 1079‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, Garin duk yai mai zafi, gabadaya baya jin dadin rayuwar shi sam, Don haka ya yanke shawarar ya koma gobe ,gobe tun bai dauki wani lokaci ba,a garin saboda bai ita jure ganin mahaifin shi a haka A ranan bai kwana gidan su ba hotel ya kama,, Da safe ya shigo gidan cikin shirin shi na tafiya, yaso yatafi batare da yayi sallama da Antysa ba, Amma sai yaga cewa zai dade bai shigo ba don haka yakamata su,yi sallama, da Assalam din shi, A bakin kofa sukayi kicibis da maryam wace ke kojaein fita siyo madu breads na break fasta, Idon shi ya kade yayi ja, kamar mara lafiya,ya wani fada, Dan Rabawa maryam tayi gefen shi ta wuce inda zata, Saidai jikin ta ya,ba,ta, cewa yana kallon ta bayan ta wuce, Maryam tashigo rungumay da breads har guda biyu, a gefen hannun ta, Anty Dije tace kagani ai nace kabari,ta dawo ba nesa ta, tafi,ba, Nan Maryam tagane cewa tafiya zai yi, acan cikin ziciyar ta sai taji tausayi shi yai dan mata yawa, Don ta san cewa hakan nada nasaba ga maganar da taji yanayi jiya awaya Bayan maryam tashiga a,gagauce ta hada mai ruwan shayi tafito dashi rike a cup, tanufo shi, Idanu ya zaro don bai tsanmani hakan ba,daga wanan yariyar May yasa yanzu take sasauta mai fiye da,da,? Bakin,ta na dan rawa, tace, gashi na hada mai ai Anty, Sai yau zata ce magana mai kama da ta mutunci tashiga tsakanin su, Hararan ta ya yi ,yace, wanan ai yai min yawa, ga kuma zafi, Kanta na kasa duke saboda bazata iya jure irin kallon hararan da yai, mata ba, Muryan Anty ce ya katse su adaidai lokacin da yake shirin karban cup din tea din Anty Dije wace je cewa gaskiya, Yusuf wanan tafiyar dai kamar ba shiri zakayi ta, Nan da nan idon shi suka canza zuwa tsantar bacin rai, Ba Anty Dije ba har maryam da ta dauko mai wani dan stol a falon su saida, taji wani iri, Yace cikin dasasar murya, mahaifina ke son kawo min matsala Anty, Yaki hakkuri da zancen musulunta na sai daga hankalishi yake yi, Duk da nasan cewa zuga shi akeyi akaina, lokacin yadan fara kokari kurba shayin da maryam takawo mai, Ammakin shi sai yaji baida mugun zafin da ya,zata zaiyi, Idon shi yadago ya kalli inda maryam take tana kokarin aje mai wata yar kujera irin ta zaman mata, hannu ta na dauke da ruwan pure water leda, Itama anty zaune takai saman farin kujerar roban da maryam ta aje mata dan nisa kadan da Yusuf din, Nan yaci gaba da fadawa Anty Dije yadda duk suka kwashe da maihaifin shi tare da sauran yan kabilar su, Yadago idon shi rinannu ya sauke su ga, maryam daniyar yace mata ta kwashe kayan tea din ya koshi, saboda bai faye cin abinci da safe ba haka, Idon ta suna a rintse tana mai jin zafin labarin da yake fadawa Anty ta, Muryan shi da taji yana cewa nagode zan tafi kada inyi rana ahanya, don gobe akwai inda zantafi indan Allah yakaini,lafiya yau, Sai ji tayi bakin ta na furta,zancen da takeyi a zuciyar ta, Kadaure da,duk wani, kalubalen da zaka samu daga gurin su saboda bara,zana ce kawai suke kokarin yima, Ko zasu iya juya ka idan sunyi hakan don kawai suyi galaba akan ka, Kawai ka bar su suyi tayi watarana zasu daina gaba daya don zasu saduda,dakan su, A,cikin mamakin ya ware idon shi yana kallon ta, yau itace ke nuna concern din ta akan shi saboda yazama musullmi dan uwan ta, Ashe dama saboda akidar addini take gwada mai wanan tsanar, tunda yaga suna dan hurda da Jibrin, sai KB ne ba su shiri har yanzu, Saida takai aya tai shiru dan kanta daga haka tajuya da nufin tabar gurin, Anty Dije ce tace mata maryam amma fa kinsan cewa mahaifin shi, ne taya zai yi mashi haka, A ladabce tace to, anty baki ganin cewa suna iya jan ra,ayin shi yakoma masu,, Murmushi yayi yana mikewa, tsaye yadan kalli inda take yace, kina ganin kamar zan iya komawa cikin su ko,? Kanta ta sada kasa saboda kallon ido da idon da suke fuskanta a,tsakanin su, Yace ai,ni na shiga ke nan insha Allah sai mutuwa kuma, Ya juya gurin Anty Dije yana mai ce mata idan Assalam ya tashi sai ta, massa sallama,shi yatafi, Kudi masu yawa yadebo daga cikin aljihun shi ya aje wa anty a gefen , yasa kai yafita, Bayan fitar shi, wajen minti uku Anty takasa koda motsi balle magana, saboda yawan kudin da ya aje mata, Maryam ce ta zo da zuciyar ta daya ta dauki kudin tafara kirgawa, Abin a tagani, yasanyata saurin dago kai ta kalli yar nata, cikin mamaki tace dubu dari Anty, Da sauri anty ta dago kai ido waje tace dari,fa Maryam,? Dan tsuke fuska Maryam tayi, tana kokarin mikawa Antyn ta kudin, Allah yakai idon yar uwar nata a fuskarta, cikin mamaki tace wa Maryam, may kuma akati, Maryam wace dama ta cika fam, tace to shi ance masa kina kwadayin kudin shi ne kokuwa, ? Cike da mamaki yar ta ke kallonta don maganar ya daure mata kai, Ban fhince ki ba inji Anty Dije, To may da,zai wani baki kudi haka, batare da wani, dalili, ba, ni wallahi ban son abinda mutum zai min gori akansa sam, To ke Maryam may ye naki aciki da har zaki dinga wanan zance, Dama tun jiya yake ce min, zai bar kudi wanda zan dinga mashi sadakar kosai da, sugar duk jumma, Sai a lokacin Maryam ta danji dadi har cikin ranta don azaton ra yagan su mabukata ke nan, shi yasa yabasu kudi, Kwana biyu bayan tafiyar shi sanan mahaifin shi yasan cewa yabar gari, Don haka ya kara daukaka fushin shi, don yasan cewa da gaske Joseph keyi yabar Christianity ke nan har abada, Ya jijiga kan shi shi kadai a zaune saman kujer da ke bakin gidan man shi, yace impossible, Waya yadauka yakira wani aminin shi dake zaune a Lagos din Yusuf wanda a lokacin yadawo agajiye daga inda suka tafi can kusan boarder, Ya zube saman kujerar dake cikin falon nashi, yana mai da numfashi guda guda Kokari yakeyi yadan sasauta aninin da ya ke saman wuyar rigar shi don yadan ji shahakat, Ido biyu yayi da wasu murda murdan katai cikin bakaken kaya da wani bakin glass a idonun su, Addu,an da yagani cikin teach your self islam da yana ce saida ya haddace yai saurin zo mai arai, A zuciyar shi yace bari ya fara gwada, wanan damar yagani, Batare da ya nuna razana daganin su ba yace LA,ILLA HA,ILLAH ,ANTA SUBBAHANAK INNI KUN TUN MINAL ZALLIMIN,,,,,,, Cikin nuna rashin jin tsoro yace masu cikin natsuwa, what's, do you want from me,? Zagayowa sukayi inda yake zaune suma suka dan zauna mutum guda daga cikin su ne ya tsaya saitin kan shi da bindiga a hannun shi yana wasa da ita tankar bawani mugun abu yarika ba, Mafi tsawo da kauri daga cikin su ne yadan gyara tsayin glass din idon shi yace, Bama son komai daga gare ka,saidai kai kawai muke bukata, yana mai nuna Yusuf din da yatsar hannun shi, Daga haka wanda ke tsaye ya sai mai wani kyale ya toshe mai hancin shi dashi, Sai farkawa yayi yagan shi a cikin wani daki mai kama da dakin gwauraye, Don yar katifa ce a kasa kawai sai wani dan tarin kaya mai kamada kayan wanki, A hankali ya bidakin da kallo cikin mamaki, yadda har suka kawo shi nan batare da sanin shi ba, Kusan minti goma sha da farkawan shi yaji anturo kofar dakin, Wasu dattijai ne su uku cikin shigar coth da wando bakake Fuskan su babu walwala acikin ta sam, sun kai wani lokaci suna kallon shi batare da sunyi mai magana ba Guda daga cikin su ne yadan rage tsawon shi kamar yadda Yusuf din zai iya jin shi daga inda yake a kwance, Yace mai ,Mr joe Y ,d u chose to live ur parents religion's, And you even go to the wrong part, A, hankali ya dago kanshi ya kalle shi tare da yin murmushin karfin hali irin ta, mayaudara yace, That's where I want my life to be,,,, Girgiza kai yayi alamar wanan yayi nisa, sosai baijin kira, Dafa mai kafada mutumin yayi yana mai cewa kada ka yi taurin kai dan samari, Bazan so ace wani abu makamancin haka yasamu daga cikin ku ba saboda ba,karamin, embraced zaka jawa zuriar ku ba, Yusuf wanda kan shi yake a duke, yadan dago kan shi cikin wata malaciyar dariya, Yace may ye na embracing acikin ra,ayin addini kuma ina, kowa abinda yake so zai yiwa kan sa zabi, Mikewa mutumin yayi ya fara tafiya zuwa hanyar kofa, Saida yakusa fita dakin yai wa sauran dake kokarin bin bayan shi, Yace masu No Need of westing our time here, Wa yan nan kaitan mutanen da suka dauko shi, daga gidan shi sune suka baiyana adakin Bisa ga umarni wa yan can mutanen da suka fita suka fara dukan shi, Sai addu,an daya iya abakin shi yake karantowa, Allah yakawo mai dauki, Ya jibgu so sai a gurin su,suka dan fita, zuwa,, shan taba waje,, Mutum guda daga cikin sune yadawo, daga baya yakawo mai ruwa a ledan pure water, A hankali ya dan duka wajen shi cikin kashe murya, yace mai I will, free soon, Daga haka yamike yai waje da sauri, gurin yan uwan shi, Can cikin dare rashin sallah da bai samu yi ba duk ya damay shi, Kamar daga sama yaji karar jiniyar yan sanda ya ji ya tunkaro, uguwar da suke, Ba,afi yan mintina ba yakama jin karar bindiga, natashi duk unguwar yakaure da karan bindiga, zat tashin hankali, Shiru yaji har nawani, dan lokaci, sai can yaji motsi alamar ana zuwa daidai kofar dakin da yake aciki, Gaba daya suka hankado dakin cikin irin hikimar su ta yan kaki, Kwance yake a daure, a hannu da kafa, shi a takure waje guda, Kafin yan wasu mintoci har sun sance shi ko, Da taimakon su, suka dan tallabashi zuwa, bakin motar, Asibiti suka wuce dashi don diba lafiyar jikin shi Alhamdullah baiji wani mugun ciwo ba sai yan kananan raunuka da yasamu kawai ajikin shi, Yusuf, yasamu sauki don har an sallamay shi bincike yanuna cewa sanadin musulutar da yayi ne yasa akai mai wanan ta,asar Saidai wai ba,a san ko suwaye ba shi da kan shi yace a kashe case din don yasan cewa yana iya samun hannun mahaifin shi aciki dumu dumu, Tun daga hospital yasa a sai, masa,ticket din fita waje, Saboda yana son yaje yadan huta har komai ya samu natsuwa, Kafain tafiyar shi yayi ta samun kiran waya daga yan uwa musuluma na kwantagora suna masa jaje dafantan Allah yakara tsarewa Saura kwana biyu ya wuce mai gadin sho yashigo yana sheda mashi cewa, yana da bako a waje, Tun daga nesa ya sheda shi ,daya daga cikin wayan nan da suka kawo mai hari ne suka sace shi, Shine mutumin da yace wa Yusuf zai yi Free din shi a lokacin da yaje a hannun su, Nan dai mutumin ke fada mai cewa, abokan mahaifinshine wa yan, nan mutane, Duk abinda yagani da sa hannun mahaifin shi aciki, Yaji cewa zasu mai dashi dan defar life shi yasa yaje ya report din su gurin yan sanda mafi kusa, Amma cewa yayi ma police yana tuhumar akwai wanda akasato a gidan nan don yana jin ihun mai shi Godiya sosai Yusuf yai masa in da yakawo alheri mai tsoka ya ba wa mutumin, Amma sai yace aa shi abinda kawai yaje bukata yasamu aikin yi, Don dama rashin abinda zai yi ne gashi da iyali, shiyasa ya shiga wanan harkan, Kwarai Joseph ya tausayawa mutumin, don yasan talauci ne yasa shi ,shiga harkan da bai dace ba,,, ZEEE MAKAWA [3/11, 10:18 AM] ‪+234 808 968 1079‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣6⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Kiraye, kirayen, sallah asuba ya kaure ko ina da musulmi sukafi yawa acikin duniya baki daya, Shima Yusuf wanan kiran,sallah na asuba ya tashe shi a lokacin, Duk da karfe bakwai na safe jirgin su zai tashi suwa, South korea, inda sonny deon yake zaune, Massalacin da ya saba zuwa, yin sallah jam,i can yanufa , Batare da jin wani shakar komai, ba ko tsoro,yafito kai tsaye,zuwa, yin jam,in, Bayan ya idar da sallah yadade, zaune gurin yana lazimi har zuwa dan waye wan gari kadan, Yana isa airport batare da bata lokaci ba jirgin su yadaga yabar kasan, don sai sun dan yi tsaye, tsaye, hanya kafin su isa, Sun dan yi nisa kdan yadauko Alkur,anin shi da Jibrin yabashi mai fassara yafara karantawa, a nutse gwanin sha,awa, kamar yadda yaji anyi bayani adinga yi, Daidai saitin kujerar shi akwai wani matashi bahaushe zaune yana ta faman dakilar wayar shi, Saurayin na hankalce da Yusuf wanda har abincin da aka aje masu baiko kalla ba sai karatun shi yake a natse, A, hankali matashi yataso saboda burge shi da yusuf yayi Sallama yai mai tare da mika mai hannu, inda yake gabatar da kanshi gare shi Yunus baba shola, daga Ibadan Nigeria amma shi ma,zauni Lagos, A, hankali Yusuf ya mika mai hannun,shi guda da ya dan dago daga karatun da yakeyi, Shimadai din fada mai sunan shi yayi cewa Yusuf Emanuel, daga, Abia, Umahia, Da ya fadi hakan sai da Yunus yakara daga idon shi yakalli kamilin saurayi mai suna biyu, Don sam natsuwar da kulawar shi ga addini baiyi kama da wanda ya fito ta wanan tsatson ba,, sam, Murmushi Yusuf yai mashi mai nuna gamsuwa da abinda zuciyar shi take tunane , akai,,, Such is life, yadan kara murmusawa,irinta gwanayen murmushi, Yunus yaciro wani dan karamin kati daga aljihun wandon shi ya mikawa Yusuf, A hankali yakarbi katin yadan karanta abinda ke jikin katin sai dan daga kai ya,kalli Yunus din, Daidai tsakiyar inda yake ya sa katin, tare da kara kallon saurayin dake tsaye har yanzu akan shi, Yace my Nice, to Meet You, Sai a lokacin Yunus ya mayar mai da kalar murmushin da yake mai tun dazu, A daidai lokacin wata yar matashiyar ma,aikaciyar aikin jirgin ta iso gurin, cikin shigar irin uniform din su, Tambayar su tayi gaba dayan su, a lokaci guda tace The You need some help,? Juyawa Yunus yayi cikin daga mata kafada yana mai cewa a,a, Shima alokacin ya koma gurin zaman shi tunda yaga bawani cikkaken ansa zai samu daga Yusuf din Sai alokacin yadan, dauki, goran ruwan da aka aje mashi agaban shi yabude ya kwankwade dukka alokaci guda, Kara komawa yayi daci gaba da karatun shi batare da ya kara kallon kowa ba, Saida jirgin su ya sauka a inda zasu fara yada zango ne , yadan fito don ya, samu dan abinda zai danci, don shi yanzu sam bai yarda da abincin jirgi na saboda bai san koda may aka hada ba, Drinks din da ya tabbatar baida surki a ciki, ya saya tare da wani dan corn dake cikin leda, Dakin da yakama acikin airport, guest house din a lokacin yadan dauko wayar shi ya kunna Miss call yaga ni har kusan guda, uku, ajere daga Anty Dije Baiji dadin hakan ba, ga shi kuma ba service anan balle yakira, Ya kai wani lokaci yana hutawa adakin yana kuma yi yana kallon agogon hannun shi, don gudun makara, A hankali ya mike da niyar tashi don shirin tafiya Card din da Yunus yabashi ce, tafodo kasa, yaduka yadauka yana mai kara bin katin da kallo kamar mai son nazarin wani abu daga katin, Can da sauri ya kara kallon katin yadan, kada kai ya furta da cewa, Alh Yunus Sikiru Shola Akani, Computers plazas, Yanzu yagane sune keda wanan katon plazas har guda biyu acikin Lagos, Yana fita suka kara hadewa da wanan guy din dasuka hadu ajirgi shi yafawa Yusuf magana cewa, Shima gaba yayi ke nan ba,a nan zai tsaya ba kenan, Duk da yagane shi amma baiyi wani daukin nuna mai cewa yasan koshi waye ba yanzu. Saboda kariyar mutuncin shi, Kusan atare suka shiga jirgi wanan katon duk da sin samu sauyin jirgi a wanan karon, Bawani dogon hira sukayi ba sosai saidai shi Yusuf din yafahinci cewa, Yunus mutum ne mai saurin saboda, jama,a, Don har yana mashi hiran cewa, tafiya zaiyi akan wasu wayoyin hannu da suke, so abugo masu irin shi, Nan dai suka dan taba hira sai gab da zasu saukane Yusuf shima yabashi nashi card din, Sosai, Yunus din ya nuna farin cikin shi akai tun ajirgi sukayi sallama tare da yuwa juna alkawarin kira idan sun dawo gida Nigeria, Ya samu, Sonny ya aiko adauke shi, kusan minti goma da suka wuce, Sunny yayi murna kwarai da ganin Aminin shi kuma abokin shi, Saida yaci abinci yakoshi tukun sannan Sonny din ya,shigo gurin shi tare da wata fara budarwa yar kabilar Koreans, Tufafin jikin ta kusan tsirara za,ace take don kusan komai nata afili yake, Sau guda yadaga kai yakalle ta bai kara ba, suna rungumay da junar su har, zuwa inda Yusuf yake zaune saman, dogon kujera, Sonny din ne ke,tayawa Yusuf fita zuwa club, din dare don more rayuwa, Kai Yusuf yakada mai alamar a,a, bazai tafi ba Sonny wanda hannu sji ke ta faman shafar budurwan shi, Yace mai akwai fa fine,fine bear, akwai kuma young bebies, agurin Fadar haka kawai da Sonny yayi sai yaji wani irin haushi acikin zuciyar shi Sonny zaicigaba da kwadaita mai fa,idar fitan,sai Yusuf cikin wani murya maikama da tsawa yace mai, You can go pls all dis is forbidden in my religion, alcoholic, ladies games, etc, Wani malalacin dariya sonny yasake yana mai cewa which religion forbids all dis things, A gadarance Yusuf yace mai Islam, Da yatsa yanuna yusuf yace you islam when,? Sai kuma yakara bushewa da dariya har yana yar tabawa cikin dariyar tashi, Hannun yariyar da suka shigo maikama da tana yawo tsirara, Yaja yana mai cigaba da dariyar zolayar da Yusuf yai mai cewa wai shi muslim nne Shiko Yusuf suna fita sai yaji kamar har yanzu dakin na warin yariyar dazu, Window's din dakin yadan sake don iska ya shigo mai, Dogayen benayen da suka cika garin masu mugun tsayi da kuma sha,awa yadan tsaya yana kallo , Bai dade gurin ba ya shiva bayi ya kara watso ruwa tare da dauro alwala don yin sallah raka,a biyu kamar yadda yagani cewa mutun yayi sallah raka,a biyu aduk lokacin da ya tafi wani bakin guri don neman sa,ar tafiya da kuma tsari,daga miyagun kaddarori, Wani jallabiya yadauko mai laushi dakuma santsi daga cikin kayan shi yasa, Yadan kai wani lokaci yana istigifar akan neman yagiyar ubangiji ga kurakuran da ya tab ka abaya, Har zuwa lokacin da barci yadaukeshi batare da yasani ba xuciyar fam da kewan mama da Ejoma Wanda mahaifin shi ya rike su can kwantagora, wai kada yaje dasu yafasu cikin irin harkan da ya shiga, watau islama,,,,,, Maryam wace, ke zaune ita kadai a gidinnwata bishiyar lim dake cikin harabar makarantar tasu, Idan ka ganta azaune zaka dauka cewa karatu takeyi a lokaci ashe sabanin hakan, Bata komai sai tunanen yadda A,A ke mutuwar nuna mata kauna, akoda yaushe, Amma sam fafir yaki yarda ko sau guda ya je su gaisa da mahaifin ta Kamar yadda Anty Dije ta bukace ta da tafafa mai yaje su gaisa da baba ko hankalinshi zai dan kwanta a yadda koyaushe cikin tambaya yake ita Maryam har yanzu ba tasamu wanda ya tsaya mata bane, ? Duk yadda taso yaje sai doje mata yake yi don kullun acikin uzuri yake na cewa, akwai abinda yake jira kafin yaje, Dafarko tazaci ko dan irin abinda zaibawa babane idan yatafi baida sai taga ba haka bane Yauma kamar baya anty Dije takara tunatar da ita akan zancen cewa yayan ta iliya zai zo yakamata yazo su gaisa da shi, Amma sai take ganin ai baidace, takara mai magana ba don tana son taga iya gudun shi, Firgigit ta zabura don jin antaba a baya. Ahankali ta sauke ajiyar zuciya don shiga yanayin da tayi, Safiyace wace yanzu zama da jibrin yasa ta takarayin wani clean, tazama budurwan kwatance acikin kawaye, Cikun murmushi tacewa aminiyar nata, A,A ko karatun,? Maryam tadan nisa tace bako daya, tana kokarin boye damuwar ta, Saida Safiya ta zauna tukun ta kalli maryam din wace ke nuna alamar ba komai dake damun ta, Maryam inji Safiya wace takurawa maryam din ido kamar mai son fahintar wani abu daga gareta, Kada ki sa zancen namijin da ba aure kukayi ba arai tun yanzu A,A dai yana son ki amma yan uwan shi ne matsalar ku, Saivs lokacin maryam tadan daga kanta takalli Safiya, Safiya tace a yadda naji ance mahaifiyar shi tana son hada shi aure da diyar dan uwata, Amma shi A,A baya son wanan hadin sam, ra,ayinshi na gare ki, Saidai ya bukaci mahaifiyar nadhi da ta yarje ma,shi yaure ku daka biyun, Maryam ta kwalalo idon ta waje tace biyu da wa, kam, Hannu ta daga tace pls Safiya ki daina wanan zance dan Allah inma har wasa kike yi, Tana kokarin mikewa Safiya ce, tadan jawo ta da style takoma ta zauna, Indan harda so wanan bakomai bane maryam ni shawarana kawai ki bi, a hankali pls, Kuyi min afuwan pls yau banda caji, ZEEE MAKAWA [3/11, 10:18 AM] ‪+234 808 968 1079‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Zaune yake a saman sallayar shi bayan ya idar da sallah asubah, Sai a lokacin yaji tsayuwar motar Sonny wanda hakan na nufin a clubs ya kwana ke nan ba a gida ba, Da yar alamar buguwa atare dashi lokacin da yashigo, Yana rataye da coth din shi a kafadar shi da yar fara,ar shi yashigo gidan yana fito, Alamar daren jiya yai mai, dadi kenan don har da yar waka yake yi, Cak ya tsaya guri guda gami da yar murzar idon shi ko duk mayen da yake ciki ke sa shi ganin haka, Tangal, tangal yadan kara karasowa inda Joseph yake zaune yana lazimi, Sai kuma yadan ja baya kadan kamar wanda yaga wani abin tsoro, Da yar babban yatsar shi ya nuna Joseph din, cikin mamaki da kuma tsifa kamar ta tsoro,, Joseph yafada da alamar tambay Are you, rely muslim, ? A lokacin Yusuf yashafa, addu,an a fuskan shi, a hankali, Kamar yadda yadafe da hannuwar asama yana addua haka kuma yadade da su a manne ajikin shi yana shafawa, Saida ya mike tsaye ya dan fito daga wajen inda yai sallah, Takalman roba ya sa ta yawo acikin gida,duk Sunny din yana kallon shi a cikin mamaki, Gurin shi ya zo yana mai dan mai wani kallon daga ina kake Iam asking you guy, ? What's you see is true am rely muslim, now, Yana mai jijiga kanshi kan alamar tabbaci babu tanta ma akai, Daga,haka ya, wuce inda,Sonny din yake tsaye saida u yadan wuce shi kadan sanan yace You, better go and sleep, or have a bath, now, Daga haka baikara ce mai komaiba yai shigewar shi kawai yabar shi tsaye sororo, cikin mamaki, Sonny yasan halin Joseph inba abinda yace mai din yayi yatafi yiba ba,za azauna lafiya ba, Ko a,da balle yanzu da ya ga yakoma Muslim sanin cewa akwai muslim da taurin kai so sai gaduk abin da suka sa a gaba, Bayan shigar shi dakin, tare da aje abin sallah dake hannun shi, Waya yadauko don yakira Ànty Dije wace miss,call din ta daya gani tun a hanya, yadan sa shi cikin kwankwanto ko lafiya, Ba,adauki wani lokaci ba mai tsawo a ka daga wayar, Saidai ko ba,a fada mai ba yasan muryan Maryam ce a layin, Sam bata gane ko layin waye ba don gani bakon laba ce kuma ta kasan waje, Cikin yar siririyar muryan ta tace Assalamu Alaikum, A hankali shima yakarba anashi bangaren da wa,alaiku,mussalam warahamatullah Sai dan shiru ya biyo baya don rashin fahintar mai kiran wayar da batayi ba, Hello din da tace yai daidai shima yana cewa, Assalam fa dan Allah, Sai alokacin ta gane cewa shine, ke magana alokacin Assalam ya tafi school tace cikin yar muryan ta, ok to abani Anty ko, ? Anty ta shiga bayi ok, kawai taji yace har zata aje wayan sai taji muryan shi Kamar a marki yana ce mata ya,school din, Alhamdullah ta furta again, Allah ya taimaka yakara cewa atashi bangaren,, Maryam mamaki yakamata, don bata tsanmani cewa yasan tana school ba ma, Maryam tana kokarin aje wayar ta,Anty Dije tafito, daga bayi tana kokarin sa hijab, ajikin ta duk da akwai ruwan wanka a jikin nata, Wayar maryam tamika mata da,sauri tana kokarin kara mata,a kunnen, ta, Waye Anty Dije ke tambayar maryam,Dan katuba din nan ne , Waye hakana, inji anty, tana mai yin sallama a wayar, Maryam kan sa kai tayi zuwa karasa sauran aikin ta kafin lokaci ya kure ma, Yusuf najin ta saidai sam bai fahinci may take nufi da hakan ba, Murmushi yayi kawai yana mai cewa, hummm, don jin muryan ta tana fadawa anty ga waya, Muryan Anty Dije,ce kemai sallama tana tambayar lafiyar shi alokaci guda, Bayan yabata ansa ne Anty takara cewa Yusuf labarin da mukaji da gaskitane cewa an sace ka a kwantagora, Wai wasu muslimi da basu son kashiga addinin su sun sace ka a Lagos, ? Murmushi mai sautin yar kara yi, don jin irin sherin da aka kullawa muslmi, No,no,no ba haka na bane Anty they said it, don su tayarwa mutane da hankali, They just want to blackmail din na ne, so that zan bar musulunci, Pls don't mind them gereh, Yakara zance adan cikin bacin rai, don yaji haushin wanan bita da kullin da suke mai haka saboda kawai ya canza addinin shi, Shin wai haka akewa duk wanda ya cazan addinin shi ko kuwa dai shi kawai sukewa hakan,ne, Maganar mutu biyu tafado mai azuciyar shi itace. Maganar Abdulsamad da yake ce mai zaka shiga ganin abubuwan rayuwa daga kowani bangare da ga yanzu, Amma sai ka jajirce wa zuciyar ka kamai da komai ba komai ba tukun, Ka kyale su duk wani barazanar da zasu kawo maka ko hari sai ka jajirce ka kalubalanci al,amarin su, Inji Maryam ke nan aranan da ana gobe zai bar kwantagora, Dan murmushi yayi acikin zuciyar shi yace har da karamar yarinya kuma mace tasan da wanan abin zai zo, Jin yadan yi shiru Anty Dije wace takai zaune a lokacin saboda girman da cikin ta yayi Taci gaba dacewa kadai yi hankali dasu pls kasan cewa a yanzu suna cikin jin haushin ka, Kasan abin da akwai cin rai so sai baka ganin a wanan lokacin ma da muke a ciki, Mukan mu musulmai a rarabe muke muna kojarin yiwa junar mu aibu, saboda banbancin akida kawai, Bayan duk abu guda muke koyi dashi sunannar ma,aiki S,A,W, Amma sai kaji, musulmi dan uwan musulmi yana kokarin kafirta dan uwan shi, Shin idan har wasu kafirai ko Christian suna son shigowa kuma sukaji yadda muke sukan junar mu a fili dakuma cikin cassette kala kala,yakaga abin zai kasan ce, Ai kawai tsoro zamu basu su dinga jin cewa mu kan mu ba,a hade yake ba, ai sai su dinga shaguber mu, su yi kokarin hana duk mai son shigowa cikin islama daga cikin su, Kawai mu barwa Allah ubangiji zabi mudai mu dinga yin koyi da,sunanna mai karfi ba tare da mun, bari yan wani addini har sunji cewa da akwai baraka atsakanin mu ba, Kawai dai abubuwan gasunan ne Yusuf Allah kawai yasa mu dace, da rahamar sa, Bai iya furta komai ba sai cewa yayi Nagode Anty, Harzata kashe waya sai yace mata kudin sadakar sun kare zuwa yanzu ko, Kai kai kai haba dai Yusuf aiko rabi ban kashe ba, aciki, Haka sukayi sallama yana mai jin wani irin kasals ya baibaye shi a lokaci guda, Sai tunane yakeyi acikin zuciyar shi, na maganganun da sukayi da Anty Dije Barci yasamu yadauke shi har zuwa wani lokaci, yasa yadan watsake gajiyar shi , Bayan yatashi yai wanka yaci abinci, a wajen shan iska yasamu Sonny zaune yana, dan shan yan abubuwan acikin wasu kwalabe, Ko bai kallaba yasan cewa abin maye ne yake sha, Zaman shi ga kujerar da ke fuskantar,wanda Sonny din yake sama, Sai Sonny yadago mai cup tare kwalbar yana mai yi mai nuni dayasha, Kai yagirgiza mai alamar a,a, baya sha saida yakai ga bakin shi ya kurba yana mai lashe baki, Yadago kai yakalli Yusuf din yace mai cikin murmushi How the you become Muslim? Dan yamutsa fuska yayi yana mai kokarin daukar jaridar da yagani asamar tebur din da suke zaune, Yace is a Long story, jo, Cup a hannun shi yadakatar da shan da zai yi yanamai kafe Yusuf din da ido, don son karin bayani akan zancen, A takaice Yusuf yace mai I just want be, Sai kawai ya bude littafin dake agabanshi yaci gaba da karatun shi, Kara tsiyaya ruwan mayen, cikin kofi yayi yana yi yana mai kallon Yusuf yana dariya yana girgiza kai, Yusuf yagane nufin shi sarai watau bai san abinda yake yi ba ke nan, Anabi din dake ire agaban shi ya tsinka ya jefa abakin shi, a hankali, Sonny dake kallon shi yana ta murmushi ganin yaci diyan Anabi din yace ma Yusuf so is true some food's or drinks are forbidden to Muslim's people, Sai yar dariya dayayi yacewa Yusuf kagan ni nan shiyasa banyarda da wani addini ba can,, Nafi son in zauna ahaka batare da wani takurawa ba yafi min, yakafa kofin mayen shi a baki yashiga kwankwada, Ckin wani sallo ya kira sunan Joseph din yana mai mai kallon serious alokacin, Stop calling me with dat name pls Iam YUSUF, Still Sonny bai yi fushi ba kamar yadda Yusuf ke mai magana a tsatsaye, Yace woow so a Nice name, Yusuf I love the name, Do u remember we have a course mate, from, Egypt with dis name, Sun dauki wani lokaci a gurin Yusuf na ba abokin nashi kuma aminin shi labarin irin halin rayuwar da yake ciki, Dakuma dalilin shigar shi cikin musulinci, So u have faith in dat, Yusuf din yana,mai kada kai yace rely, Agogon hannun shi da yadan daga yadubu shi ya nuna mai ko karfe nawa, Ba bata lokaci ya mike zuwa dauro alwala, don ya gabatar da sallah magrib, Duk a binda yakeyi Sonny yana tsaye a jikin bango ya harde kafa yana kallon Yusuf din, cikin mamaki, Azuciyar shi yana tunanen har yaushe ya fara islama da zai iya wanan abin dayaga sunayi time to time, Daidai lokacin da Yusuf yai sallama yadaga hannaye shi sama yana addu,a zai shafa yaji a na taben hannaye a bayan shi, Cikin mamaki ya juya Sonny ne tsaye, yana mai dariya ya na tafawa, Yace so Are so serious with dis religion,? Baima magana yadauke carpet din shi da yake sallah akai, yashige da abinshi, ciki don gudun kada wani najasa ya haukai, Kwana biyu dayin haka suna zaune suna cin abinci ,rana kira yashigo a wayar Sonny, Saida yadauki tissue, ya goge bakin shi da kyau sannan yakai hannu ya dauki wayar, dake kara sabon kira, Sabon noba yagani wanda bai san may shi ba , da mamaki yadauka yana kallo a hankali, Bayan gaisuwa shiru yayi yana sauraren mai magana daga dayan bangaren cikin natsuwa, Idon shi suka sauka akan Yusuf wanda shi ma alokacin ya gama cin abinci yana goge bakin shi, Abinda yaba mai maganar dashi ansa yasa Yusuf saurin dago kai ya kalli Sonny din, Sonny ke cewa shi canza addinin shi ba matsalar shi bace iyakar haduwar su dama ta friendship ne, yazama masu amin taka Don haka shi bazai iya sa Yusuf ba yadaina abin da yake so kamar yadda shima Yusuf bai isa ya hana shi irin rayuwar da yake so wa kan shi ba Wanan is a personal matter not a business or a deals, Daga haka ya dangware wayar ya na tsaki batare da ya kalli gurin da Yusuf yake ba yatagi fuuu, yabar gurin, Mamaki kan Yusuf yayi matukar yin shi da wanan bita da kullin da ake mashi, Bayan fitan Sonny a dining area din Yusuf yakai dan wani lokaci zaune yana tuna Mikewa ya alokacin yanadan tako acikin dakin yaje ya dawo, Yana tunanen wanan hali irin na mutanen su da basu da yarda da kaddara, Sai alokacin yafara tantance tsakanin kafirci da imani,a musulunci Yanzu yagane cewa,ko dan karamin yaro musulmi yafi katon kafiri imani, Sannan ga sauki ga musulunci duk dadewan ka wanda bai sallah koda kakai shekara dari, ne Duk ranan daka ce ka karbi kalmat shahadda duk zunuban ka sun wanke kadawo daidai da musulimi dan shekara dari, Hannayen shi rungumay abaya yatsaya cak don tuna wani abu da,yayi a zuciyar shi,,,,,, A gajiye yau maryam tadawo daga makaran ta duk da tasan cewa akwai aiki agaban ta na girkin dare, Amma bai hata wurgat da jakarta gefen kujera ba tafa saman gadon Anty Dije Tana mai cewa wash Allah na Anty tun safe banci komai ba wallahi Ga abinci can ki dauko ki ci mana, Wayyo ni Allah anty abincin baya wuce wa saboda dadewar danayi banci komai ba, Saidai dan abu maidan ruwa ruwa pls,? Takarashe fadi tana mai kashe ma Anty ido guda alamar zo laya, Tana wani lankwashe kai kamar zatai kuka, Anty Dije tace, cikin murmushi,, to,gashi maryam banda wani abu mai ruwa bayan tea, Sai ko drinks din da Yusuf yasiya muna kafin yatafi, Nako san baki sha, abinda yafito daga gare shi, ke Tunda Anty ta fara zancen ta maryam wace ke kwance,wai tana exercise din bayan ta,, Tamike zubar dan jin inda maganar Anty Dije ya dosa, Anty Dije tana yin shiru,,maryam ta dan langabe kai ce, hai Anty wanan dane fa yana kafiri, Cikin kwarewa da iya iya shagwaba ta furta zancen kamar wace zatai kukan gaske, Dallah ja cen kunya bai isheki ba wallahi Maryam, inbashiba wai yau kece da cewa hakan, Maryam kan mikewa tayi alokacin ayadda takejin son shan drink's komai zata iya,daurewa, akai,,,, ZEEE. MAKAWA [3/7, 1:14 PM] ‪+234 803 381 3188‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,, Yusuf yadan samu natsuwa sosai a zaman shi tare da Sonny saboda shi Sonny ba mutum bane mai son shiga har kan wani, Wanan damar da yusuf yasamu yasa,shi samun sakin jikin shi har ya manta daduk wani tashin hankali dayaje ciki, Ganin yau jumma,a ce juma,a biyu kenan bai samu yin sallah jam,i ba Don haka yasa a ranshi cewa yau zai shiga gari yadan zagaya don yadiba ko zai samu wani guri da musulman garin ke yin sallah jumma, din, Tun ranan Thursday ya shirya cikin shigar wasu kanan kaya kamar yadda yake yi kulun, A daida, fita ta wajen gidan, suka hade da Sonny wanda ke shirin shigowa, Kallon mamaki yaiwa Yusuf din yana mai tambayar shi ko ina zai tafi haka, Ba boyo ya sheda mai cewa ga inda zashi searching din gurin bautar su na ranan Friday ne, Haba joe in ji Sonny yakamata ka fada min sai mu fita tare in taya ka dibawa, ai hakan zaifi katafi kai kadai, Zuciyar yusuf tayi fes jin abinda Sonny yace yasan kuma har cikin ranshi yafada, Basu sha wani dogon wahala ba sosai don wani abokin hurda Sonny musulimi suka kira shi yai madu kwatancen gurin suka tafi, A zahiri idan kaga gurin zaka dauka wani, ma,aikatace sai dai in kashi ga, Sundawo gida Yusuf na cike da farin ciki har bai iya boyewa, Sonny ya fahinci haka sosai inda ya yake tunanen irin yadda wanan addinin yai tasiri aran Yusuf cikin lokaci guda, Saboda yasan Yusuf din sosai lokacin da dukkan su suke bearing din Christianity Baibada wani munhin manci akai ba kamar wanan yadda ya ga time din sallah su five times a day baya wuce joe din, Shin wai su muslim din nan wasu irin mutane ne masu karfin zuciya haka da taurin rai, akan abinda suka yarda dashi, Basu dawo gida ba saida suka biya gurare da dama aranan, inda Yusuf yai yan sayayan yan abubuwan bukatun shi indan zai dawo Nigeria, Washe gari tunda safe,Yusuf ke ta shirin shi na zuwa massalaci batare da bata lokaci ba yafito cikin shiga mai daukar hankali, sai kamshi ke tashi ga carpet din sallah shi da yar karamar tasbaha a hannun shi yarika, Da mamaki Sonny ke kallon shi don shi har ya manta zancen zuwa mosque yau, da Yusuf zai yi, Amma sai yaga ashe cewa shi Yusuf din bai manta ba abin na zuciyar shi, Tausayi sosai abokin nashi yabashi sanin cewa yayi nisa sosai ga wanan akidar, Al,amarin sai ya burge Sonny kawai, don ya yarda da mutane ke cewa wai islam is a teitorim religion, Sai ya fahince cewa rayuwa ce ta saukake, aciki babu takurawa juna ko sa ido ga harkan wani, Don haka shi da,kan shi ya bukaci kai Yusuf din, mosque, aranan, Motar shi maikyau mafi tsada suka shiga inda tun a kusan haraban gurin zakaga irin yadda maza da mata da yaran su ke ta dandazon zuwa gurin bautar nasu, Kowa kagani cikin shiga ce ta alfarma ko ina lif a rufe daga mazan har matan su, Gwanin ban sha,awa gaduk wanda yagan su, kowa kula dan uwa tankar yan ciki daya, Sai zuwa wani lokaci mai tsawo suka dawo daga, massalacin daka kalli Yusuf kasan cewa yana cikin annuri, aranan, Saboda yadda yake ji tankar andauke mashi wani nauyi ne arayuwar shi, Sai yanzu yake tabbatar wakanshi da cewa ba karamin sa,a yayi ba nafitowa daga cikin kafirci cikin duhun kai, Indan har su wa yanda sukayi zamani da Annabi Isah yan uwanshi da yan yaren shi da akasa su yarda dashi da sakon shi, Suka kan su sun tabbatar dacewa akwai wani wanda zaizo bayan ahi Isah din kamar yadda yake da magabata agaban shi (watau, annabawan da sukazo kafin shi) To su yanzu da suke bin akidar Christianity don wa sukeyi tunda an fada masu a littafin su cewa zai zo, Hannun shi yadaga yashafi sajen shi dake kwance a fuskan shi lif, Yana mai hamdalah acikin zuciyar ashe afili har da hannuwar shi yadaga sama yashafa, Sonny wanda ke kallon shi mamaki yakara kamashi sosai sai ti yake yi yana dan satan kallon Yusuf din, Wanda ahalin yanzu yaga yadda yaimai wani irin kwarjini Washegari da safe, bayan ya idar da sallah yazauna yayi irin addu,oin da yasaba yi, Gurin yin exercise yadan fita har zuwa lokacin da gari ya washe sosai, Sanan ya,shiga wanka yafito ya hau tebur don yin break fast, Sonny yafito cikin shigar zuwa office yadan zauna tare, Yusuf suka karya nadan wani lokaci, Yusuf din ne ke fadawa Sonny yana son ya koma gida don ci gaba da harkokin shi don gudun kada su tsaya mai duk da yasan ba abinda zai faru insha Allah, Sonny mamaki ne yakama shi sosai yace yadawo ya zauna kusa da Yusuf din yana mai ce mai, May zai sa bazakai zaman ka anan ba, kawai ka share kowa, Don har na fara maka planing din din abin yi don ka kauda zaman banza, Amma ni naga kawai gara kabar zancen komawar ka yanxu har zuwa wani lokaci zai fi, Yadan dafashi yana mai cewa ya daure yaba su, dan time tukun kafin ya koma, Wanan zance na Sonny abin dibawa ne sosai don hakan zai sa su dan fita zancen shi, Amma kuma baya son yabar harkokin shi na can gida, sam Don haka yakira KB da Jibrin tare da,wani babban amin nin shi amanar kulawa da harkokin shi in secret, Bayan wata guda daga can ya wuce saudiya ya gabatar da aikin umurah, Yaji dafin wanan tafiyar tashi so sai don yakara yin hamdallah da rayuwar shi, Sosai suke business kamar a gida Nigeria suke, don Sonny mutum ne wanda bai ma natare da shi keta sam, Ba karamin riba yasamu ba daga wanan zaman da yayi acan Gashi ya murje yayi kyau yayi dan jikin jin dadi ba mai muni ba saboda yawan exercises, Alhamdullah Anty Dije ta sauka lafiya,tasamu Da namiji wanda bayan sati akasawa yaro sunan Abubakar Sadiq, Wanan sunan yaiwa maryam dadi sosai kasancewa suna A,A dinta ke nan, Sosai akasha buki sai kace sabon haihuwa ne kamar na farko, Inda Jibrin da KB suma sun zo har gida sun,wa Anty Dije barka Shi kanshi maigidan wanan haihuwar ba karamin dadin shi yaji ba don ga haihuwa ga samun girma daya yi agurin aikin su, Kayan goyo sosai yazo wa maijego da jariri da inda har dangin shi suka dan fara tsegumi akai, Wai ta tare guri taki bari wata ta shigo itama tadan lakaci arziki, Sai ita da yan uwanta ke cin abin su, ita dai bata biye masu ba sai harko kinta take yi kawai, Anci ansha sosai agurin kamar yadda yakamata a duk wani taro, Sai washegarin suna bayan an watse ne baba yazo da kamshi don ganin jariri Maryam ce ta dauko mashi shi cikin showel, fari kal, Bayan an gagaisa ne baba yaiwa yaron addu,a tare da yiwa uwa fatan gama shan ruwan zafi lafiya, Sai dan shiru yabiyo baya, alokacin ne yadan dago kanshi cikin fuskan damuwa yana cewa anty wace ke tsugune gefe guda saman wani dan karamin kujerar mata, Ya zancen maryam ne wai yaji shiru, dafarko yaji zancen rigirigi yanzu kuma yaji sakwot, Dije yakamata ku mai da hankali kinsan dai in badon a gurin ku take ba ba,zan barta har takai haka ba ba wani matsayi Don ni bokon bandauke shi wani abu mai muhunmanci ba ga diya mace, Har wasu yan uwa na acan gida suna ganin kamar cewa nine ke ra,ayin tayi karatun bokom Kinsan yadda nike da yan uwa na duk da bawai wani arziki ke gare ni ba amma ganin ina acikin gari har yanzu akwai hassada a tsakani na dasu, Anty Dije ta dan gyara zaman ta datayi mai kama da tsugun ni ta fuskanci baba da kyau, Tace baba gaskiya muma bamu so akai war haka batare da wani matsaya ba akai, Da farko ya nuna muna agaskiya baizo da wasa ba, Katseta baba yayi da cewa To aimu,bamuga alamar hakan ba, saurayi yadade tare da budurwa har tsawon wani lokaci amma babu wani magana mai karfi aciki, Gaskiya Dije idan har bazai wani motsa ba yakamata kufita zancen shi kada kice zaki biye wason ran yariyar nan, Kodai ba yanzu za ai auren ba to ya motsa ma na asancewa,yana ciki, Ya turo da manyan shi su shiga cikin harkan hakan zaisa kiwa yasan matsayin sa, Daga anty har Maryam kansu na duke akasa don jin maganar da baba keyi acikin bacin rai, Daga haka yamike yana cewa kunji maganata ke nan nafada maku nagaji da surutun mutane haka,har aciin iyayen ku ke Dije ina shan surutu, Itama Anty Dije mikewa tayi alokacin tana cewa baba yayi hakkuri insha Alkah komai zai zo karshe badadewa ba, Har baba ya bargidan kan maryam yana kasa aduke, cikin ladabi, Daren ranan Maryam bata samu yin wani barcin kirki ba kamar yadda tasaba gatada karatun test nan da kwana biyu, Saboda maganar tazo mata abazata don bata tsanmaci baba zai yi wanan zancen ba, Washegari haka ta tashi bawani kuzari atare da ita saida Anty taimata magana sannan tadan sake ranta, A makaranta duk yadda taso taboye wa safiya abin bai yiyu ba, Don haka safiya sai taji kawai itama bataji dadin ganin aminiyar cikin damu ko yaushe kan zance guda Gaskiya yau zata fada mata gaskiya cewa ta rabu dashi kawai takama masu zowa son ta da gaskiya,. Don ko a kwanaki wani abokin Jibrin yai masa zancan ta, Zaune suke a cafeteria su na son dan shan, drinks, Maryam wace ta dade da lulawa duniyar tunane, ko bata ko san ida suke ba a lokacin, Safiya tadan mata kyatci da hannu a fuska tadanzabura kamar wace taji tsoro, Dan ajiyar zuciya ta sake tare da kallon safiya din tana kokarin kako murmushi, Safiya tadan kai mata harara cikin murde fuskanta, Wai Maryam mayke damun ki hakane pls,? Tadan gyara zaman ta,tace bari kawai safiya wallahi ina cikin damuwa, Tun jiya da baba yazo muna barka haihuwa,, Dakata Maryam, wallahi ki,yiwa kan,ki fada ki danai irin wanan dogon tunanen kadafa ki jawa kanki matsala ina fada maki kullun, Akan namijin daba ki tabbatar ko zaku zauna tare zaki halaka kanki, Tadan kara nisawa tace ,baba yazo jiya yaiwa anty Dije tas akaina, Maganar baba tajiya yasa nakara sanin cewa, A A ba sona da aure yakeyi ba kawai dai,yana son amfani dani, ne ya nunawa duniya, Don haka maryam da kullun aitawa yar uwata fada akaina, Gara kawai in rabuda shi in huta Allah yabani wani yafi min safiya, Subbahanallahi maryam kada kuyi saurin fadar haka mana, Nan da nan idonta yakawo hawaye, kamar zatai kuka, Wallahi safiya hakan yafi min don bazan yarda kullun mahaifina yaita bata ranshi akaina ba,, Dan shiru sukayi a tsakanin su, nadan wani lokaci Safiya tace kenan kina nufn duk son dakikewa A,A ya tashi abanza kenan,? Saida ta share kwalar da ya silalo mata tukun sanan tace, Gaskiya kan safiya rabuwa dashi zaifi min Yanzu ke maryam bazaki canza shawara,ba akai, Ki tunkare shi kiji may yake ciki akai, ? Maryam ta katse Safiya da cewa , Wani, ? Allah ya kyauta min, shi bai mun magana aure, ba nice zan masa, Kawai dai fita batun shi, zanyi, yafi mun, A,a maryam sam gaskiya, bai kamata muyiwa A,A haka ba kada mu kasa mashi uzuri pls, Muzo mu kamashi da laifin daba tashiba shi baima san yayi ba, Yanzu dai musan yadda zamuyi kafin lokacin don musan mafita Amma dai kin san bazan iya tun,karanshi da wanan zancen ba, Kadafa ki manta har yaya illiya yakirashi kan zancen amma sai ya doje kawai, Shine yanzu kike ganin nizan iya tunkaran shi da wani zance can, Kenan ma nice mai son ya aureni bashi ba,, Kai gaskiya duk zancen ya,daure min kai wallahi, Amma ki barni dashi kawai zan san yadda mukayi dashi, Sam bazan nuna mashi cewa ma kin san da wanan zancen ba, Maryam takara goge hawayen da ya kara makale mata tace nagode kwarai safiya da wanan shawarar taki, Haba maryam kifi karfin haka fa agare ni mayye na wani godiya bayan duk yiwa kaine hakan, Safiya tace daga gobe zan insha Allah zan tunkare shi, Shi ko A,A yadauka duk gajiyace tasa maryam rashin shigowa school yau, Saida wani ke ce mai ai yaganta ta shiga napep zuwa gida yadauka malam din bai shigo bane, A,A yai mamakin ji cewa Maryam tashigo school ya batare da tai mai waya ko ta iso inda yake ba, Don haka ba bata lokaci yadauki waya ya kira ta,yanamai tambayar ta ko da gaskakene yau tashigo school din,? A dakile taba shi amsa da cewa eh, kawai ta kashe wayan ta zuviyar ta na mata kuna, sosai, Mamaki fam a zuciyar shi don tunda yake da maryam yauce rana ta farko da ta taba mai irin haka, Wanan abin yai matukar bashi mamaki da daure mai kai alokaci guda don sam bai kawo komai ba sai tunane, may ke faruwa,? Dadare yazo gidan su amma sai tace ace mai bata nan kawai haka yasa yakara rudewa, Washegari Safiya ta samay shi a office din shi yana zaune yana aiki acikin computer tar shi yana saye da riga shirt mai dogon hannu fara,bakin wandon Jean's a jikin shi, sai yar farar glass da ya manna wa idon shi, Da sallamar ta tashiga office din nashi yana ganin ta yadan yi murmushi yana mata iso data shigo, Bayan sun gaisa ne safiya ta fara shedawa A,A yadda mahaifin Maryam, yasa ta aga ita da yar ta duk dadewanan nan Shiru yayi har zuwa lokacin da takare zancen ta da cewa mahaifin maryam ya dibar mata wa,adi, Hankalin shi a tashe yake batare da yaiwa Safiya magana ba Itama dai din kallonshi takeyi, don ganin irin reaction din da ya shiga lokaci guda, Saida yaji ta tana huce da iskan bakinta yadan gyara zaman shi yana cewa, Safiya, wallahi duk na ma rasa may zan ce dake, Sai kuma yasoma share zufa duk da sanyin A,C dake office din nashi Aiko magana zakayi don musan mafita, daga cikin Yadan ce cikin marairaice murya, wallahi safiya akwai abin da nake planing akaine, shiyasa, Bawai sharewa nayi ba yadda kuke nufi, ba Safiya tace malam ba fa wai aure akace kuyi yanzu ba fa Kawai da ka gabatar da magabatanka suga iyayenta don manya su shiga shiga cikin zancen, Saida ya kara share, fuskan shi karo na barkatai, Safiya tace kaga aure sai lokacin da katashi ke nan, Yace nasan da haka safiya amma abin dibawa anan shine kokari nakeyi ingama abubuwan dake gabana tukun Su kwantar da hakalin su bawai zan yaudareta bane,o something like dat, Kawai dai zan samu, illiya idan yazo muyi magana akai, Safiya tace malam idan har bada magana mai karfi zaka je ba kada katafi pls, To safiya idan sun min haka basuyi min adalci ba gaskiya Kallon shi safiya tayi da mamamki, Tace malam waiko kasan duk maganar da kayi da mahaifiyar ka ranan da kukaje da maryam gaida ita duk a kunen maryam ne Ido waje yake kallon safiya da mamaki da kaduwar jin zancenta, Nan dai takwashe komai tafada mai wani rin nauyi da kunyane suka lulube shi lokaci guda, Safiya takare zancen ta da cewa malam don Allah kada k bawa maryam, baya ka guje ma,ta Sai kuma sai zuciyar ta yai sanyi tana batun sa kuka, Tamike tabar office din batare da ta saurare shi ba,, ZEEE. MAKAWA [3/7, 1:14 PM] ‪+234 803 381 3188‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,, Alhamdullah Yusuf ya kammala wani course da yadan kara tsayar da shi kasar Korea, A harkan business ne dama ya tsaya don kara ita fasaha akan, kasuwanci Don haka yanzu kimanin watan shi takwas ke nan rabon shi da kasar shi, Duk abinda yakeyi yanzu hankalinshi yakoma gida Nigeria musan,man kakar shi wace yabar ta kwantagora, tare da Dad din shi, Saboda yasan cewa babu shiri atsakanin su saboda banbancin churches din su, da suke bi, Yasan cewa yan church din su Dad basu kaunar mabiya Olumbo, Sonny ya na hankalce da Yusuf din duk kwanakin nan baya son walwala sosai, Lafiyayyen abinci tare da abin sha daga yayan icce,aka hada masu a matsayin dinner yau, Sai da Yusuf ya idar da sallah shi na isha,i tare da,shafa,i da wuturi, Sanan ya koma yai wanka yafito cikin shirin shi, Yayi mamaki Kwarai da ya samu Sonny a zaune yana jiran shi,, Yusuf yadan bashi hakkuri tseda shi da yayi har zuwa wani lokaci, Cikin daga hannu Sonny wanda,yake saye da wata far coth da wandon shi fari, sai bakar shirt da yasa daga ciki, Yadan, dago wa Yusuf, hannu alamar ya share ba matsala, kawai, Nan suka zauna suka fara cin abincin su hankali a kwance, Saida suka dan dauki lokaci batare dayin wani magana ba sai karar cibin da suke cin abinci kawai kake ji yake tashi,agurin, Sonny ne yadan dago kai yakalli Yusuf wanda dabi,un cin abincin shi yanzu duk ya canza,ba kamar da ba can, baya, Murmushi mai sauti Sonny yayi wa Yusuf wanda hakan yasa shu dago kan shi yana mai kallon shi,, Sai kuma ya daure fuska acikin yar damuwa yace, Man this your religion is good, and have a nice characters, Unlike Christianity, Da sauri Yusuf yadago kai ya kalle shi, Yace ma Yusuf man see how yo pray everyday, Bayan yawan sallah da kuke yi a kullun, batare da damuwa da ko kowa ba, alokacin yinta, Amma su Christian saudaya kawai suke zuwa church a cikin sati, inda wasu ma bawai dole su tafi ba,, Littafinku mai tsarki muslumai dayawa sun haddace shi a kan su , Littafin ku mai tsarki Alkur,an, yana nuna abu guda ne ga kowani irin yare za,a fasssara shi, Zaku iya shiga kiwani irin massalaci kuyi salkah aduk lokacin da ta riske ku Ba kamar Christian ba suda da angan ka sai an tambaye ka wani church, kake zuwa a cikin sati, Idan kafadi wanda ba nasuba, zasu iya bata rai, dakai afili, Dazaran ance kai musulumi to daidai kake dakowa daga cikin musulmi, kuma a nuna ma so da kauna alokaci guda, Sai kuma duk abinda ka iyayi dazaran kace Allah shikenan an yarda da zancen ka,kowace iri ce, Amma su Christian dazaran kace God zaka zama abin zargi ke nan in ma bakai hankali ba sai antara ma taron,mutane, A bincike ka, wani irin God, kake zance shi god din yan Catholic ne ko god din Anglicans, kona na living faith, kok, shin na deeper, life, Duk da su ma musulmai suna da wayan nan akidodin a tare da su amma sai kayi nisa sosai a cikin su zaka iya ganewa, Amma su kan Christian a filli suke nuna nasu, Zaka iya jin ance maka ai jabun pastor ne wani Banda musulumai da ko yaya imanin ka yake zasu iya binka sallah, a jam i Gashi su musulmai aduk lokacin da suke azumin su na watan ramadam mai tsarki, duk duniya zasu sani sanan sauyi zaizo wa kowa daga musulmai har Christian alokacin wanan azumin Amna baka taba jin wani abu maka mancin haka acikin bautar Christian, Idan wani abin al,ajabi yafaru musulmai zasu yarda da cewa daga Allah, ne amma su Christian sai su ce wai in Jesus, name, wasu kuma suce karfin shedan ne, Zaka ga idan mai wa,azin musulumai yana waazi, musulumi koda karamin yaro ne ya kewaye shi yana saurare har zuwa lokacin da za,a tashi koda kuwa mutum nada abin yi alokacin ba zai tafi ko ina ba, ko fitsari azasu yarda su tagiyi ba don kada afadi wani abinda basu ji ba,, Idan ka lura da musulmi yana girmama pastor afili, badon komai ba sai don sanin cewa shugabane na addini, Amma,su Christian suna jin haushin limamen musulumai sosai, Yadda zaka ga musulmai suna girmama shugaban nin su sai kaga su Christian suna kokarin gardama da pastor cin su, Kai abubuwa da dama nayi searching din su naga akwai bambanci halaiya so sai a tsakani, Tunda ya fara dogon sharhin shi Yusuf yadakatar da cin abincin da yakeyi yana mai tsura mashi ido, Acikin zancen Sonny din Yusuf yagano cewa akwai wani magana mai muhin,manci, da Sonny din ke son yi dashi, Hakan yasa ya tatara hankalin shi gabadaya yana mai sauraren shi, Yyana kaiwa karshe sai ya kalli Yusuf da kyau ya aje cokalin da ke hannun shi a cikin plate din da yake cin abinci, Yakara duban Yusuf din sosai, yace a yar fahintar da nayi yanzu Joe nagane cewa muna da banbancin addini sosai ni da kai, Kaga zancen mu hada harkokin mu kamar yadda muka saba ada bai taso ba , Kagane ko? Yusuf yace,, Fadi maganar ka kawai ina sauraren ka ai,, Sonny yadan girgiza kai yana mai cewa don haka na yanke shawara nakuma rubuta komai a rubuce har an sa min hannu, cewa Nabar maka duk wasu kaddarori da suke a hannun ka saboda nasan cewa kana bukatar taimako yanzu a rayuwar ka so sai, Nayi hakane don in kareka daga duk wani barazanar da za,a yi kawo maka na cewa zasu iya gurgunta ka daga cikin har kokin ka, Wata irin karfafan ajiyar zuciya Yusuf ya sake da yaji wanan zancen na Sonny, Fuskan shi dauke da alamar damuwa mai fayyace mamaki aciki, Magana Yusuf din ya fara cikin wata irin murya mai ban tausayi don duk mamakin wanan hukuncin na Sonny ya ruda shi,, Kawai sai yaji Sonny din ya kaure da wani mahaukacin dariya alokaci guda,, Sai kuma ya koma ya tsuke fuskan shi ya fuskanci Yusuf din karo na biyu yana mai kura mai ido cikin ido, Yace may zakace min Joe, koka manta cewa da taimakon ka muka kai wanan matsayin da muke aciki ni da abokina Inda Allah bai hada mu da kai ba ka dage har saida kaga mun gama karatun mu aida ba mu kai haka ba, ko ? Mikewa yayi ya zagayo har zuwa kujerar da Yusuf yake zaune yadan duko yarankwafo zuwa gare shi yana mai magana kamar cikin rada, Yace , don't say thanks pls,? U deserved it Yusuf wanda kanshi ke a duke don jin zancen yake tankar a mafarki, Ya dan dago kai ya kalli Sonny din kara na biyu cikin mamaki, Murmushi na gamsar wa Sonny din yai mai alamar eh, Haka suka tashi gurin inda Yusuf kewa Sonny adduan fatan shiryuwa hanya madaidaiciya , Batare da sanin Sonny ba Yusuf ya gai,yato su jibrin tare da KB inda sukazo mai tare da,Abdulsamad, Saboda yanzu suyake ji tankar yan uwan shi na jini, Sunyi mamaki sosai irn dinbin dukiyar da Sonny ya tara a kasar mutane haka bayan ga kasar shi can na haihuwa suna bukatar shi, Sun yi wa Sonny godiya sosai dafatan kara samun daukaka a dukiyar shi, Shiko sai mamakin irin yadda suka dauki joe tankar dan uwar haihuwar bawai kawai saboda addini suke nuna mai haka ba, Sosai Sonny yaji dadin zuwan su inda ya mai dasu kamar wasu manyan guest din shi, Satin su guda sukadawo gida cike da farinci, dakuma alheri mai yawa, Saida Yusuf ya tabbatar da cewa komai da ya turo su Jibrin da shi da KB sun kammalla mai Sannan ya fara shirin komawa gida Nigeria, tare da karfin gwiwa atatare da shi, Ànty Dije ce zaune a saman tabarman robar da ta shimfida a,waje saboda zafin da akeyi a garin tankar rana zai dafa mutum, Gefen ta Abubakar ne a kwance cikin net na yara yana barcin shi hankali kwance, Maryam ce ta fado gida a daidai wanan lokacin, cikin gajiya tashi gida da sallamar ta a bakin ta, Anty Dije tadan daga kai, takalle ta gami da ajiyar zuciya, Tacd don Allah maryam, huta kidan taimaka min muyi aikin nan, Maryam wace tanawo wani farin kujerar roba dake aje a gefe guda, ta zauna, Tace wai Allah ana dai zafi gaskiya, sosai shi yasa yau ma banko tsaya jiran safiya ba na sa kai kawai na wuto, Kallon ta Anty Dije tayi cikin yar tuhuma kamar zata daure sai kuma ta kasa Tace shi A,A din ya daina dauko ku ne yanzu,? Maryam wace tambayar yazo mata a bazata, Shiru tayi saboda ta rasa ansar da zata ba Anty Dije a lokacin, Kara maimaita tambayar tayi wa yar kaunar nata, Wacce dama duk kwanakin nan tana lura da bata acikin walwala tun lokavin da baba yazo da zancen ta, Dan hawayen da take kokarin makalewa, ne yadan digo daga idon ta, Ki tashi ki dauki abinci kici inji Anty saboda ta fahinci, cewa kuka kaunar nata take shirin yi, Tausayin irin hanlin da yar uwan nata take ciki takeyi Saboda ta san cewa tana cikin wani hali saboda so, Maryam ta share hawaye ta da bayan hannunta ta mike zuwa cikin da kunar su, Kallo anty Dije tabi bayanta dashi tana mai mata fatan alheri a rayuwa, Fatan dai Allah yai wa Maryam din zabi na alheri, a rayuwa, Tunda maryam tashiga ciki tana zaune, a bakin gadon ta ko, takalma bata cire ba akafar ta, Wayar ta dake a cikin jakar ta ce tai kara alamar kira, Kamar ta share kamar kullun saida tace bari yau ta dauka taimai kashedi ya daina kiran ta kwatakwata, Cikin wani irin murya mai birkita maryam a duk lokacin da taji shi, Wanda yasa gaba daya duk maryam din ta rikice, alokaci guda ta rasa duniyar da take, Wani irin taji aranta na yadda sam bazata iya fada mai maganganun da ta shirya fadamai ba, Maryam ta saki wani irin ajiyar wanda shima A,A din yaji kamar yazo inda maryam din take alokacin yabata hakkuri duk da irin kunyarta da yake ji, Shima A,A din anashi bangaren ajiyar zuciyar don jin cewa maryam din tadan sauko daga fushin da ta dauki lokaci mai tsawo tana yi dashi, Yakara cewa cikin wata irin murya ransarauniya maryam yadade ga A, A gaban ki tuba yake yi, Murmushi ne ya subuce mata tai shi a hankali, duk yadda taso tai magana alokacin ta kasa, Yace Maryam ina fatan zaki bani dama in zo in maki bayanin irin abin da ake ciki, Shiru tayi saboda sam bata san may zai ce mata ba idan har yazo din, Tasan dai bai wuce yace mata kawai tayi hakkuri ya aure su su biyu kamar yadda safiya tace yace,, Wani irin ajiyar zuciya tasake tace, idan zuwar naka bazai zai haifa min alheri ba kawai kabarshi Yar dariya tayi irin ta mazan da suka san kan su, Ya Allah dai ya kai mu anjima ki dubi hanyata nagode, Idan ta ta lumshe tanamai jin wani iri atare da ita Ajiyar zuciya tayi mai fitar da sauti tana mai bude idon ta, da suka sauka a saman na Anty Dije,,,,,, ZEEE. MAKAWA [3/7, 1:14 PM] ‪+234 803 381 3188‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Yan uwa musulmi barka mu da jumma,a , Ubangiji Allah yasada mu da Rahama da Albarkan da ke cikin wanan ranan, Allah ka yafe muna kurakuraren mu Allahuma Ameen,👏👏👏👏👏👏 Sanye yake cikin wasu, fararen coth, da wani, farare, takalma rufaffu, kayan sun karbi, jikin shi, sosai, sai idon shi dake saye da dan farin glass karami, A hankali yake ta,kowa daga matakalar jirgin, guda ,guda, hannun shi,guda yana cikin aljihun wandon shi, Jirgin su a airport din Lagos ya sauka, inda masu taron shi suka zo,, Gurin screening yanufa batare da wani bata lokaci ba akai mashi, duk wani screening yadda yakamata, Daya daga cikin driver s din da suka zo daukan shi yakar bi wata yar case da ke hannun shi, Bawani bata lokaci su,kabar airport din shi da wa yanda suka zo tariyan shi, Sannu a hankali yakarewa gidan shi kallo gidan da yakewa kallo tankar wani sabon guri da bai taba zama ba, Saboda gyaran da ya turu da kudi akai mai, Anan falon ya zube saboda yana tare da gajiya, ba abin da yake bukata sai ya dan watsa ruwa ajikin shi, Ko zaiji dan karfi karfi ajikin nashi, kafin ya samu dan abin da zaici, Motsin da yaji ne ya sanya shi saurin daga kai, don ganewa idon shi kowaye, Hakan yai daidai da Ejoma, wace ke sauko daga wani dan steps da yafito wani part na gidan, Da saurin ta tazo daniyar rungumar shi kamar yadda su ka saba idan yadawo koda gurin aiki ne, Da sauri yadan jaye jikin shi daga gareta amma yana mai,mata murmushi, Dan yaron dake rike a hannun ta ya daga sama cikjn wasa yana zagaya da shi, Sauke yaron yayi yana mai kallon Ejoma wace ke saye da wani bakin buje da yafitar mata da surar bayanta baro,baro, gashi dan guntu, daidai iya katarar ta, Ejoma ce tafara magana bayan taga ya, sauke yaron daga daga shin dayayi, Tace brother we don base, woo, Shima murmushi yai mata yana cewa where my grandma ? Grand mother dey for village since, tree months ago, Murya kasa kasa yake tambayar ta ya akai haka , Ejoma tadan tabe baki tukun sai tace, You know Dad no dey allowed her to go to her church, A dan tsora ce ya dago fuska cikin mamaki da jin mamakin zancen ta, Saikuma ya maida mamakin nashi zuwa dan murmushi mai sauti, saboda tunawa, da sanin kowaye mahaifin shi, Fuska kumshe da murmushi yace ma Ejoma is alright, i, will go and seen soon, Daga haka ya haura zuwa sama inda dakin shi yake don yadan watsa ruwa, Cikin daga murya Ejoma ke cewa brother your food is ready on the table, Yakai wani lokaci a sama sannan ya sauko daidai lokacin da Ibrahim shima yashigo gidan, don taron shi, Duk atare suka taru suka ci abinci, gabadayan su, Tsab ya mike yashiga wani dan bayi dake makale a cikin makewayin, Alwalar sallah azuhur yadauro alokacin amma saboda gajiya nan ya tsaya a falo saman sallaya, Addu,oin da yajeyi bayan sallah ne ya gabatar alokaci har tsawon wani lokaci, Brother are still bearing the Muslim, Idanu ya zuba mata don mamakin kalamin ta, saboda yaji abinda tace kamar a mafarki, Don haka ya shafa addu,an shi ya fuskan ce ta, da kyau, Gyaran murya yayi yace mata dama ana canza addini ne anyhow,? Sai ta girgiza kanta tace ba haka bane kawai dai taji Dad na cewa evils spirit din da suka shige shi har ya juya zuwa Islam, An, kore su dakarfin addu,oin pastor's masu yawa daga cikin pastocing su, Wani iri Yusuf din yaji a cikin zuciyar, wanan maganar ya kasance mara misaltuwa agare shi, Shin dama ashe har yanzu Dad naga bakar shi na cewa sai ya canza addinin shi da yake ra,ayin yi a rayuwar shi, Gaskiya zai dauki wa Dad duk wani mataki da yakamata yadauka wanan karo, Ai bashi kadai bane, dan shi yafara zama musulmi, da zai ce ba zai hakkura ba , Koda kuwa Dad din zaiyi barazanar kwace mai duk wani dukiya da ya mallaka a rayuwar shi batare da yabar mai koda kwandala ba, Ya tuna da labarin da Abdul samad yabashi, na,wani matashi , da yai zamani da manzon Allah S,A,W Maisuns Mus'ab Ibn Umair, matashine, mai ji da kanshi a cikin garin makka, Matashin ya fito daga wani family mai karfin arziki sannan,sannan ya kasance dangata sosai daga duk wani matashi na zamanin, A wancan lokacin kaf samarin Makkah suns jin jins mashi wajen ado, don ko turaren ma dayake amfani dashi alokacin abin kallo ne, Sannan mahaifiyar shi takasance mai tsananin sonshi wanda hakan ya haifar da shakuwa mai karfi gaske a tsakanin su, Tufafin da Mus,ab Ibn Umair yake sawa, da takalmin shi masu matukar, tsadane so sai, A lokacin da manzon Allah SAW ya fara wa,azi da kira ga mutanen makkah akan subi addinin Allah, watau musulunci, Yawan wa,azin da yake saurare daga Annabi yaji ya gamsu zai shiga addinin islama. Hakan yasa ya fuskanci tsanani da azaba da rashin galihu, Inda yakoma yakassnce tankar almajiri, duk wanda yaganshi bazai gane shine shiba Dan yadda ya koma ma abin tausayi don hatta suturar jikin shi duk sun yayyage, Sai watarana mahaifiyar shi tace ya kai Mus,ab kadawo vikin addinin mu kafita,wanan addinin na islama, da kashiga Amma sai Mus,ab yaki suka dinga azabatar da shi azaba mai tsanani, amma yaki ya tsaya akan addinin shi na islama, Daga karshe ya koma gurin Annabi Muhammad, (SAW), Ya hakkura da duk wani daular duniya da ake kwadaita mashi, anan Yusuf yanisa ya waiga inda yake tsaye a bakin window, Yace a ranshi kida Dad zai kwace mai duk wani abu da ya mallaka bazai fita cikin addinin islama ba, Shi yanzu yasan cewa yafi karfin duk wani barazana da mahaifin shi zai mai akan dukiya, Kwana biyu kawai yayi da hutawa, ya shirya don zuwa ya dibo, kakarshi wace bai san halin da take ciki ba a yanzu, Ba karamin tausayi matar yake ji ba a matsayin ta na wanda, ta rage mai yake gani kamar uwar shi, Tana zaune ta mike kafa a saman wani tabarman roba, a gefen da dan inwa yakai acikin gidan nata , Sai ganin shi tayi kamar a mafarki don sam batayi tsan manin cewa zata kara ganin shi arayuwar taba , Tadade rungumay dashi a jikin ta tana kuka tana wani gwalanci irin na yare, Sai kuma komay ta tuna tasake shi da sauri tana ta tatabashi kamar tana tuhumar ko ba shi bane a gabanta, My child are still in that religion ? Mumushi yayi ya jawo goshinta ya man,na da nashi yace mata Even you mama you will joined me, very soon Dan tura shi tayi baya yawuce tangal, tangal kamar zai fadi, Dariya tabashi a yadda yaga tanayi don daga hannun ta tayi tana wani kewaya shi a saman kanta tana cewa over my death body, Komawa tayi ta zauna tana wani bubuga kafa wai ita tayi fushi, Direct wuce yayi zuwa cikin dan falon ta na ginar kasa wanda saboda tsufa har yana batun zubewa, Photo mahaifiyar shi ce yai tozali da shi, wace ke saye da wani zanin irin na matan IBO,ta daura wani dankwali daurin gwagwaro, Murmushi takeyi da aka dauke ta kamar zatai magana Yadade yana kallon photo yana maiji dama ace ta musulunta ka fin ta mutu, Shigowar grandmother, yasa,shi barin gurin zuwa saman tsofin kujerun dake falon, Itama zama tayi saman kujerar dake gab dashi, tana mai mai kallo cikin da muwa, Shine yafara magana yana mai tambayar ta may yasa ta dawo kauye da zama, Bayan tasan cewa babu wani wanda zai kula da ita anan yanzu, Yace ga gidan shi can abirni babu kowa aciki mai yai hana taje can ta zauna, Saida mama tadan waiga kamar akwai wani gidan wanda zai ji abin da zata fadi alokacin, Tadan kara gyarazaman ta har kusa dashi tace, That your father is very wicked, He can killed person, woo Nan take sheda mai cewa bayan tafiyan shi taji mahaifin nashi na waya da wasu cewa a kama Joseph ai masa duk wani horo da ya dace dashi don yadawo cikin Christianity, Murmushi yai mata don dama yasan cewa shine ke turowa ai mai wanan wulakancin, A ranan Yusuf bai yarda ya kwana wanan dan kauyen da yar tsohuwar ba dawowa sukayi tare, Inda taga duk gidan ya canza mata saboda gyare,gyaren da akayi wa gidan, Sosai gidan ya canza mata cikin dan lokaci har ta rasa gane ko ina ne part din ta na da,, Ganin Ejoma da tayi tazo taron ta yasa ta gane cewa lalai agidan shi suke, Wanan karon sosai ya shirya ma shiga garin na kwantagora Badon komai ba sai don ya tunkari mahaifin shi wanda ke ta yi mashi bita da kulli, Motorcine har guda uku yatanada don wanan tafiyan,da yake son yi kafin ya fara harkokin gaban shi, Saidai wanan karon ba,a gidan mahaifin shi zai saukaba kamar yadda ya saba, Hotel lafiyayye aka kama masu tun kafin su iso garin, Har abincin da zasu ci an tanadar masu shi, KB ne yai wanan hidimar, Zaune take tana kwalliya a bakin mirror saboda tana expecting din zuwan A,Adin ta, Muryarda taji yana sallama tuni zuciyar ta, ta tsinke Zabura tayi saye a dan tsorace, tadan saurara ko kunnuwar take mata karya, Bashi bane a zahiri don sam ba su tsan manin cewa zai zo a wanan lokacin ba, Muryam Anty Dije ce ya kara tabbatar mata da cewa shi din dai ya shigo, Inda taji Anty na tacewa sannu da zuwa Yusuf Kaine tafe babu ko labari, zuwa balle a shirya ma,zuwan naka, Wani murmushi yayi mai sauti yace bana son ku wahala ne ai shiya sa ban fada maki ba, Sigar dayake magana kawai zai tabbatar ma da ya kara samun canji a rayuwa, A,hankali yake karasowa zuwa inda anty take dauke da Abubakar a hannun ta, Ya saye da wani yadi mai laushi baki ajikin shi sai wata yar jar hular dara dayasa wa kanshi, Gadan gadan yanu yau,fi inda take da yaron dagani duk hankalin shi na gurin yaron, wanda bai taba gani ba, sai Cak yadauki Abubakar yafara dan wasa dashi ,daidai gitowar Maryam wace kamshin ta kawai kawai, zai saka gane tafito, A hankali ta iya furta mai sannu da zuwa,daga haka tasa kai da niyar fita kawai, Gabantane yafadi saboda ganin yadda Yusuf ya canza gabadaya cikin lokaci guda,,,,,,, ZEEE. MAKAWA [3/7, 1:14 PM] ‪+234 803 381 3188‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, Yusuf ya canza gaba daya ya wani murje yayi fari sosai da yar jiki daidai shi, Wasa ya keyiwa Abubakar yana cewa wanan little friend din bai sanni ba , ama baka kai abokina kyau ba,, Muryan ta na rawa ta iya furtawa Anty ta cewa zata dan fita, Sai,dai kuma Yusuf din yadan tare hanya ta daidai inda zata dan wuce, zuwa waje, Yaro nai yai sallama yace wai ana sallama da Maryam a waje, Maryam da ke shirin fita hanya kawai take nema takumaji muryan Anty ta nacewa dan Allah maryam dan dauko wa Yusuf kujerar roba a waje, Maryam wace dama a cike take don tasan cewa A,A yagajine har ya turo yaro, Don yana zaton ko ta manta dashi a waje saboda motocin da yagani a kofar gidan su yasa,shi, zaton baki sun masu yawa ne, Batare da tai magana ta juya tanufi inda kujeru suke aje a,dan wani kwanar da fridge din su na waje yake, Kanta ta kawar gefe har ta isa gaban shi,ta ajiye mai kujerar, cike da jin haushi ta aje mai daidai inda yake tsaye, Yana yawan dagula mata kwanciyar hankalin ta idan ya na a gari, Ya zauna a hankali yana mai cewa bissimillahi, azu,bikalamatillah tammah Kafin Anty ta takara sata yin wani abin da saurin ta tabar, gurin, Tana shan kwana suka hada ido da Yusuf yasakar mata wani tsadadden murmushi wanda duk duniya ba mai mata irin shi, sai Yusuf amma ta kasa gane ko ta may ye, Saidai da yake tasan cewa, murmushi wani part ne na rayuwar shi sai kawai ta share zancen Kanta kawai takawar gefe cike da kara jin haushin shi, Kafin ta karasa ficewa sai ga muryan Anty Dije na cewa, Ki dauko mai ko ruwa mana maryam kinsan cewa, ba wuta falon da zafi, Murmushi da yafitar wanan karon mai sauti ce don har Anty taji shi, Komawa tayi cikin wani irn bata rai kamar bata taba dariya ba arayuwar ta, A cikin tire ta jero, kayan shan har da da su cup, A gaban shi ta ajiye kayan, shan tasan cewa idan bata zuba mai ba Anty zata kara kwafsa mata dole badon taso ba ta dan duka don ta zuba mai, Kamshin turaren BUSSHIRAH da ta shafa ya gauraye ma hanci har saida ya yar ajiyar zuciya, Muryan yaron dazu ne ya ratso kunnen su, yakara sallama yana cewa wai yace tazo don ba dadewa zai yi ba, A lokacin Maryam tai yunkurin ta mikewa, sai ji tayi yana cewa ta karbi Abubakar daga hannun shi, pls Sosai suka shaki numfashin juna tare da hada idon su a lokaci guda, Maryam ce tai saurin kauda kanta gefe tana mai jin wani irin abinda bata taba jin shi ba arayuwar ta,, Babu shiri tabar gurin da sauri daga haka tafita zuwa kiran da A,A ke mata, Sai zuwa dare, ya shirya zuwa gurin mahaifin shi, saboda bazai iya kwana a garin batare da ya tafi ya gan shi ba, Mr Emanuel yana zaune tare da abokan shi su biyu da suka zo mai hira, Kasan,cewar shine mai hali acikin su dan sauran basu kai shi arziki ba ko kadan, Duk idan an fara labaran NTA shiga yakeyi don kallo da sauraro,abinda kasa ke ciki, Don haka sauran abokan hiran nashi suka mike zuwa gidajen su, A kofar get din gidan suka ga shigar su Yusuf, tare da guards din shi, Motocin suka bi da kallo inda hankalisu yabasu cewa shine yazo gari, Sunji haushin barin gidan da sukayi batare da ya iske su a ciki ba,, Yusuf din ne ya fara fita daga cikin motar da yake acikin ta, yadan dade tsaye da kofad motar rke a hannun shi kamar mai nazarin wani abu Saidai a cikin zuciyar shi addu,a yake yi na neman rinjaye daga ko wani irn masifa da zai riska, agidan Tunda motocin suka tsaya Samuel dake zaune a saman dining table ya mike tsaye,yadan leka tagar falon nasu don yaga kowaye, Cikin murna ya ce "Ah, brother Joseph,, har ya mike kamar zai tafi sai sukayi ido biyu da mahaifin nasu wanda ya watsa mashi harara dole ya koma ya zauna, A, cikin takon shi mai kama da ta kasaita, yashigo falon Idon shi cak ya sauka ga na mahaifin shi wanda alama ta nuna cewa, ya cika fam, a ida yake jira kawai yake yi ua fashe, Da harshen su na yaren, IBO ya gaida mahaifin nashi, wanda ke zaund daure da wani katon zani na atamfa da akayi shi kamar buje, Kallo guda Mr Ema yai wa dan nashi yagane cewa har yanzu yana nan daram a cikin addinin Islama, Mr Ema wanda tun dan nashi bai shigo ba ya nasa cewa zai falfale shi da masifa in har yana cikin Muslim har zuwa yanzu,, Amma suna hadda ido sai yaga yaron nashi ya kara mashi wani irin kwarjini a fuska, Har yaji cewa bazai iya ba amma dai karfin hali irin na kafiri, balle Mr Ema mai hali kamar na kafiran farko,,,, Cikin kakausar murya, yafara wa dan nashi magana kamar haka, Wai kai may kake nufi da zuwa gurin mu bayan kaba mu baya, Yanzu mai kazo bida a gurin mu da har za ka,shigo min gida kai tsaye batare da izini na ba Addinin naku bayace mutum bai da ikon shiga gidan wani batare da izini ba, Joseph kabani mamaki kabani kunya a idon duniya, Duk so da kaunar da na nuna maka acikin diyana sakkaiyan da zakai min ke nan, Karasa addinin da zaka shiga sai addin musulunci addinin da yake na yan ta,addah, Kafita kabar min gida na muddin kana cikin wanan addinin baza mu taba shiryawa da kai ba, Duk da nasan cewa kana ganin kamar a yanzu kana da arzikin ka to ina son ka sani cewa gidan maina da kake harkoki dashi a Lagos na karbi abina,ko Sai katafi gurin yan addinin ka suyi maka,contribution din sadaka subaka jari idan zasu iya, Yakare maganar ko fadane yana huci kamar zai fashe, Saida Yusuf yaji mahaifin nashi yadajatar da masifar da yakeyi ne, Sai ya saki wani irin ajiyar zuciya lokaci guda yadago ida nun shi a hankali ya dubi uban, Yace Daddy kayi hakkuri da abinda kagani that is my Destiny, I can't change it, Wasu kwalaye guda biyu masu kyau ya ciro daga cikin wani dan leda, Ya taka har zuwa gaban Daddy din wani kwali dake daure da wani zare ja kamar na gift, Ya fara aje wa a gaban daddy din ya dago kai a hankali cikin ladabi yace ma mahaifin shi wanan keys din gidan manka ne komai da yadangace shi yana a ciki, Sai na biyu dake daure da wani blue din zare again, yafitar shima a gaban daddy din ya aje again, Mr Ema wanda yake tsaye sororo yana ma dan nashi kallon mamaki da tsana, Yaji muryan Yusuf din yana cewa wana wasu kudine da ya diba daga cikin kudin mai din a na sarrafa su a wani fanin to shi ne yahado kudin gaba daya har takardun business din, suna a ciki, YUSUF yadan sunkuyar da kan shi yace babu saura komai nashi a hannun shi, yanzu, Saboda addinin shi ya haram ta mashi cin dukiyar shi, Aiko Mr Ema ina wuta yasaka Yusuf saboda wanan ce damar da yake hange da zai ja ra,ayin Yusuf din da shi, Sai,gashi Yusuf din yana sanar dashi cewa wai addinin shi ya haramta mai cin ko kwandala daga dukiyar shi, Jiki a sanyaye Yusuf ya juya dan barin falon cikin kunar rai yake tafiya saboda irin kalaman da Dad ke fadi, Sa kai yayi yafita tare da yiwa falin wani kallon mai kama da ta karshe,, sai kuma ya waiga inda su Samuel da Ruth suke tsaye cirko cirko, Kawai sai ya juya da karfi alamar shi kan ba,zai iya barin addinin shi ba komai zai faru ya faru Amma yayi sallama da rayuwar kafirci da suke ciki har abada,, Yusuf na daga labulen falon zai sa kai Ruth da Samuel suka sa wani irin kuka mai ban tausayi suna cewa "Brother pls don't go, Brother come back to us pls we don't want to loose u, Tsawa Mr Ema yadaka masu saboda takaicin, da kukan su ke kara mai saboda yasan cewa yayi rashin dan shi na kwarai, da yake da shi, Yana magana yana biyu bayan Yusuf din wanda ko waigawa baiyi ba tunda yasa kai, Sai kuma ya koma ya zube a saman kujerar dake a bakin kofar yasa wani irin kuka mai sauti, Shima dai Yusuf din yana shiga mota ya sa kyalen dake hannun shi ya goge hawayen da yadan gangaromai a fuska, Drive yaja mota a hankali yabar harabar gidan, A cikin dakin hotel din da suka sauka yake tsaye yana kallon titin da motoci ke zirga zirga akai tankar rana ce ba dare, Muryan Dad ce ke mai yawo a kwakalwa yana cewa, Saboda kai Joseph nasha kunya nasha takaici kasa banda mutunci acikin church din mu gabadaya, Wasu ma ko gaisuwar arziki bamayi dasu sabo suna ganin cewa ban fi karfin family di na ba,, Ka nemi kudin ka ka gina gidan ka barmin nawa,wanan ba naka bane,,, Murmushi irin ta takaici yayi yace watau dama Dad ta wanan hanyar yaso ya kamashi ke nan ko,? Allah yasa ya samu Sheikh ya warware mashi wanan matsalar dake damun shi tun tuni, Muryan yan kan,nen shi yaji suna kukan kiran shi yadawo kada ya tafi ya bar su pls, Wa yan nan maganganun da ya ke tunawa sun sa shi ya shiga cikin damuwa da, wani tsananin tashin hankali sosai, Nan da nan idon shi suka canza kala saboda damuwa, Guri ya samu yakai zaune yana mai hada hannaye shi biyu guri guda, Yadan tallabo habar shi da su yana dan bubuga kafar shi a kasa a hankali, Tunanen da yazo mai gamay da yan uwan shi ya,sa,shi mikewa da sauri, Sai washegari yasamu shiga cikin gari gaida mutane, Gidan Abdulsamad yafara zuwa ida suka dan dauki lokaci mai tsawo suna tataunawa, a tsakanin su, Yana tashi ya wuce sai gidan mahaifan Jibrin inda suka nuna mashi jindadin irin yarda yake girmama su Yakawo Alheri mai yawa yai masu, Wasu dattawa ne zaune a kofar gidan su jibrin idan rana yai zafi anan suke taruwa kagin ai sallah azuhur, Kudi ya debo adadin da bai,san ko nawa bane ya basu don su raba, Daya daga cikin su daya yake kwance yamike zaune yana tambaya dangidan waye ya basu kudi haka, Sai cewa guda da ga cikin su yi, ai yaron nan tubabben nan ne, Au to shine wanda ya tuba din nan, dan gidan katon Arnen nan maigidan mai hanyar Lagos, Duk wanan maganar a kunnuwar Yusuf akayi su duk da yaji daci a zuciyar amma afili sai ya daure yana murmushi kawai, A daidai zai shiga mota suka yi kicibis da Sadiya Mohammad joda Karo na biyu kenan suna haduwa da ita,tun,da ta ganshi sai duk tashiga,,rudu saboda Allah yasa mata masifar son shi, Itace tafa ra gaishe shi cikin rashi kulawa ya amsa mata, Ya dan bar uguwar su Jibrin ke nan Kiran Aisha yashigo wayar shi Sam yarasa may yasa bayason lamarinta yanzu tun bayan muzuluntar shi Yake kokarin jabaya ga alamarin Aishan saboda sam baya son abinda zai sa sa a sabawa Allah ubangji Ce mata yayi zai koma ne yau ko gobe kawai amma sai bai son ya fada mata gurin da yake don kada ta cin mashi,,,,,,, ZEEE MAKAWA,,,,,, [3/7, 1:15 PM] ‪+234 803 381 3188‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Saye take da wani leshi mai ruwan kwai, (yellow), mai laushi, anyi mai yan ada da wasu duwatsu blue, Dinkin buje da riga akai wa kayan sun dane jikin ta har surar jikin ta yafito fili, A cikin sauri take shiri saboda, zata kamfanin Bobi ne yau don diba jikin mahaifiyar ta kamar yadda baba ya umurci Anty ta barta ta tafi, Saidai ya umurta da kada ta tafi sai yazo tukun, Ganin baba bai zo ba yasa Maryam din cire hijjab din ta don ta dai taimaka wa yar uwar nata da wasu ai yuka, kafin ta wuce, Da sallamar shi ya shigo gidan kamar yadda ya saba yi tun bayan musuluntar shi, Aguje su Assalam da Issalam suka dake wa Abubakar wasa saman kujerar falo Suka rungu may shi yana murmushi yafara kokarin daga su sama kamar yadda ua saba yi masu, A kunyace maryam ta gaishe shi saboda kayan da ke saye a jikin ta, Yasha Voil mai kalar ruwan fari, kal, ajikin shi,wacce ke ta faman kyalli, da daukar ido,, Kan,ta mayar kasa, cike da kunya don kallon da sukayi na hada ido a lokaci guda, don kada ya zata ko shi take kallo, Saida ya shiga falo yazauna saman kujerar dake facing din kofar ta yadda duk wand ya gilma zaka iya ganin shi daga ci, A hankali yakewa yaran yan tambayoyi gamay da school da kuma rashin zuwan su makaranta yau, A tare suka hada baki suna,cewa ai yau weekend ne har da little mummy ma yau bata zuwa, Shigowan Baba da yayi ne cikin yin sallama yana mai neman Anty Dije, wace ta dan shiga cikin babban gidan su maigidan ta, Cikin damuwa Baba ya fara magana yana cewa, Maryama tun dazu ina can gurin bidan dan kudin da zakiyi kudin mota da kuma wanda zaki dan sai masu tsaraba, Tunda ba,a zuwa gaida mara lafiya hannu sake amma ban samo wani abin kirki ba dan kudin da duk nake bi bashi tun jiya nake bi ko zan dan samu wani abu daga ci,,,,,, Bai,kai ga karasawa ba Yusuf wanda ke zaune a falon yafito don su gaisa saboda Assalam ya fada mai cewa ga baba tsoho nan, ya shigo Sai yakasance Baba din nata ma Maryam bayani a lokacin, Maryam tace Lah baba dama kabar shi ai Anty ta bani kudin mota ko , Kai kawai dama nake jira don kace kada in tafi sai ka shigo A,lokacin Anty Dije tadau dauke da wani bakin leda mai giwa a hannun ta, Cikin yar fara,ar ta take gaida baba tana cewa yanzu ake ce min ga ka can ka shigo yanzu, Dama na tafi ne, in dan samo mata abinda zata rika, Allah yai maku albarka in ji Baba yake sawa yaran nashi, Wani iri Yusuf yaji don jin yadda Dattijon ke ta sawa yaran shi albarka akan dan abu kadan, Ina ma ace shine yasamu irin wanan mahaifin mai sawa diyan shi albarka haka, Muryan Dadtijon ya katse mai yar tunanen shi yana cewa, A ina , ta, shiga mota ne Dije, ? Anty Dije tace dama cewa nayi ta tsaya a bakin hanya kamar zai fi, A,a a,a inji Baba yace tashiga ta cikin gareji kawai yafi sauki don shiga mota bakin hanya ai hatsari ne Dije, Baba yace idan kin tafi ki gayar muna da mahaifiyar taki Allah y bata lafiya Duk suka amsa da Ameen, Harda Yusuf wanda ke zaune a falon yana jin su,suna mai bashi sha,awa Daga haka Baba ya fita suna, ta ce mai baba sai anjima inji su Assalam, Maryam ce tafito daki acikin shirin ta tasa dan gyale blue,ta yane fuskanta,sai wasu yan takalma, suma blue daidai adon duwatsun Lecce din jikin ta, Cikin dan siririn murya,kamar kulun taje sallamar yar nata, Yusuf dake zaune tare da su Assalam suna hira yana jin su, amma hankalin shi yana gurin su,waje, Muryan Anty Dije cikin tausayin yar kaunar nata wace take ji a lokacin kamar su tafi tare, saboda basu san halin da mahaifiyar nata ke ciki ba, Duk da bawai sun saba da mahaifitar nata bane amma sai duk ta damu tun da baba ya fada mata cewa mahaifiyar ta bata da lafiya, Ànty Dije tace cikin murya mai rauni, maryam tsaya mana ga Yusuf ya kaiki tasha ko, Maryam wace har takai kusan kwanar fita cikin gida alokacin, Tace wa yar nata ai da ta barshi kawai sai in hau mashi a sauke ni, Assalam da Issalam ya umurta da su tashi su raka little mummy, Yaran na murna suka fito waje cikin dauki kowa na kokarin saka takalman shi a kafa, Maryam, wacce a lokacin har taku sa isa kofar gida sai ji tayi yace wacce gareji ne za,a kaita wai ? Anty Dije tace, inda zata samu motar zuwa kamfanin bobi, Ok garej na hanyar Minna ko,? Motar ya nufa a,lokacin da ya budewa yaran gidan baya suka shi itako tai kamar bata gan su ba sai kokarin tare mai mashin takeyi, A gabanta ya tsaida motar ya bude mata gidan gaba gefen mai zaman banza, Su Assalam dake bayan motar ne suka dan leko suna ce mata little mummy, kishigo, muje Sai a lojacin tadan daga kai tasaci kallon Yusuf wanda tankar hankalin shi na gurin sai tin A,C din motar, Ba yadda ta iya dole ta, bude gaban motar tashiga ta na mai wani kauda, kai gefe, guda, Basu yi wani nisa da uguwar su ba yadauko wayar shi yana tuki da hannu guda guda kuma yana kokarin bidan nobar waya, A cikin harshen IBO yake magana da mai, shi wanda ya kira da suna, Uchenna, Abinda zata iya jiya ce rice, akwaiyiro ho ,oil and anything good for makeurimo,hauw,, Jin yaren da yakeyi ne wani iri kamar ba magana yakeyi ba, yasa ta kara kauda kai tana mai jin lokacin da,Issalam ta kamo mata kai ta bayan sit ta rungumo ta, Haba Issalam ki daina mana kada ki shake ni pls, Gidan wani mai na saida petroleum ya dan Parker motar shi kamar mai jiran wani abu, Ganin da tayi sun dan kai wani lokaci gurin tsaye, yasa ta fara kallon agogon wayan ta, Lokacin kusan karfe goma na shadaya na safe saura rabi, Karar, wata mota ce kewa Yusuf, horn ,p, p, p, p, Waya ya dauko yakara yin yare, su na IBO yana cewa Emba, ok akwarihu, moi,duwobo, Daga haka taga sun karkata motar su zuwa saman titi sunbar gidan man, Suko yaran dake baya sai rawan wakar daya sa ke yi na wasu diyan larabawa, Gani ankusa kaiwa kofar shiga tashar motar da zasu kaita yasa maryam fara gyara rolling din gyalen ta tana kokarin daukar yar jakar ta dake gefe, Fiwww suka wuce kofar shiga cikin tashan, abinda yabata mamaki har takai ga waigawa ta kalli Yusuf wanda ke dukan sittiyarin motar yana bin kidan da yaran kewa waka, cikkn harshen larabci, cikin nuna rashin damuwa, Sai kawai batare da ta ankara ba taga sun share kwanar Barack sun doshi babban titin zuwa minna, Abinda yasata sake wani irin ajiyar zuciya wanda bata san lokacin da yafito fili bba, Tafiya yai nisa baka jin komai sai sanyin A,C da gauraye motar kowani sako,cikin motar, Gudu yake shararawa kawai abin shi, duk da sanyi yadan takura mata amma bai sata yin magana ba, Sai ma dan waigawa da tayi bayan motar danjin yaran dake bayan motar sun yi shiru, Barci sukeyi gaba dayan su amma a dan takure saboda yawan sanyin motar, Da an rage madu wanan sanyin kada yasasu mura tace batare da ta kalli gefen shi ba,, Saida yai kamar baiji taba zuwa can sai taga yana dan rage karfin A,C din a hankali, Wani abin da maryam ta dan lura dashi shine wasu motoci da guda ke gaban su guda baya, Amma da yake tasan cewa hanya ce tazuwa har abuja kaduna kano da sauran su sai kawai ta share taci gaba da kallon, dajin da suke ketawa, Shiko sai gudu yake shararawa abinshi cikin ko in kula, Cikin yan mintina kadan sai gasu, a cikin garin kamfanin Bobi A hankali ya fara tafiya ganin cewa sun shigo cikin gari a lokacin, Dan sassauta murya yayi yadan waigo ta yace ta ina ne gidan yake, Zaman ta tadan zakuda kadan tashiga yimashi kwatancen gidan ,a hankali sai kawai gasu a kofar gidan, Kamar ko yaushe mutum ya je zai iske mutane zaune agidin iccen cediyar dake kofan gidan, Maryam tasha mamakin ganin motocin da suka jero tare ashe wai tafiyar su guda ne, A gidin wasu itace lim dake gefen wani guri kamar daji suka Parker motocin su, Sai a lokacin maryam da wani nauyi ya lulubeta dan kunya, Ta,iya furta nagode a hankali Bakomai yace lokacin da yake kokarin ganin su Assalam dake bayan mota akwace, suna ta kwasan barcin su hankali kwance, Kafa guda tafara fitar wa waje inda kafar ta guda ke cikin motar,tana kokarin daukar yar jakar da tasa tufafin ta aciki, Suko mutanen dake a kofar gidan gidin icce hankalin su naga motocin don suga ko su waye suka shigo , Maryam na,dago kai da niyar ta fito sai gani wasu murda, murdan kaita tagi har mutum shidda tsaye a kofar motan Gaban ta ne yaba da dam, dammm, saboda ganin irin yanayin shigar su, Kwantar da hankalinta tayi ta fahinci cewa tare da Yusuf suke don ganin yadda suke kokarin rike kofar da ya bude don ya fito, Kusan a tare suka fito daga motar tana kokarin saba hand bag din ta dake dauke da kayan ta kala biyu kacal, Sai a lokacin ta fuskance shidaga inda take sukayi ido hudu kafin kiftawa da bissimillah takawar da nata, Bata san may yasa ba take jin nauyin shi bata jimirin kallon shi, Nagode takar furtawa cikin kwantar da kai, sai kuma tadan leka mota tana kallon yaran dake barci acikin motar, Allah tsare hanya takara fadi kamar wace bata son furta hakan a hankali, Daga haka ta sa kai zuwa cikin gidan kawai batare da ta saya jiran komai ba Jama,an gidan sunyi mata sannu da zuwa tare da nuna jin dafin su daganin ta, Dakin mahaifiyar ta tawuce direct don ganin bata waje alokacin, Can take kwance ta kuryan dakin ta saman wata kodaddiyar tsohuwar katifa duk ta latse, Ga tarin tsumakara birjit a ko, ina saman katifan, dake akai, Dan wani tsohon tebur dake dakin dauke da wasu kwanoni irin nada daban daban, Sai kuma wasu buhu,hunan hatsi dake jingine a gefe an,dan rufe su da wani tsohon tsuman ragar zani, Kwarai maryam ke tausayawa mahaifiyar nata wace ke kwance ko kai bata iya dagawa sosai, Wasu mata mutum biyu suna daga kofar dakin suna cewa aiko ke maryam anga sauki yanzu sosai, Ai kwana biyu da suka wuce baki ko iya tsayawa ashe,? Muryam mijin mamace kecewa ku kauce ga baki nan shigowa,dan Allah, Maryam tai kokarin aje jakarta asaman wanan tsohon tebur din, da niyar tadan fita bakin su shigo, Idon,ta cak ga Yusuf wanda ke rike da hannun su Assalam, Mamaki nauyi kunya duk suka taru mata a, lokaci guda, Daga kofan dakin kokari yakwyi ya cire takalmin shi masu tsada dazasu iya kai kimanin kudi dubu hamsi ko faye da hakan, Wata daga cikin matan taje tadauko mai kujera yar tsugunno na mata ta aje mai ta kofar dakin daga ciki, Dan bashin dake tashin dakin shigowar Yusuf sai dakin ya gaure da kamshin turaren shi na maza, THE,,, Sannu mama ya jikin ki Allah yabaki lafiya,, Yace acikin hausar shi dake nuna cewa shi yare ne bawai pure hausa ba, Wani kara sukaji jep, alamar an sauke buhun abinci a gurin da mamaki Maryam ta dan leka don ganin ko may ye a gurin, ake ajewa, Buhun shimkaface yar gwaunati da na su semovita, sai su kwalin sabulu, da omo harda jarkan man gyada data manja, Da sauri ta daga ido ta kalle shi wani malalacin murmushi ya sakar mata, Sai ya,dan daga kai ya kalli inda mijin mama yake tsaye yace mai may ke damun tane haka,,,?? ,,, ,,,,,,,,,,,,, ZEEE MAKAWA,, [3/7, 1:15 PM] ‪+234 803 381 3188‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Malam mijin mama yadan gyara tsuwar shi yadan kalli inda Yusuf yake zaune Assalam yana saman kafar shi, Yace wasa wasa wanan abin tafara mata har sai,da ya kaita kwance daga karshe, Yanzu dai an wanke mata makoshi ko zata iya cin abinci, koda kadan ne yafi zama haka nan, Maryam wace ta kurawa mahaifiyar ta ido cikin tausayi don tasan ba karamin wuya tasha ba daga kwance, Gashi babu wani kulawa na kwarai da take samu, da ganin yadda ta koma, Muryam Yusuf ya dan dawo da ita dai,dai, taji shi yana cewa,mijin mama, May likita yace, sai da yai dan murmushi sanan yace andai kaita,gurin chemist an mata allura biyu, Dan iska yafitae a bakin shi batare da ya kara magana ba yai shiru, Tari mama tati mai kama da sarkewa, Da sauri maryam tai kanta kamar zata, fadi tadan tallabo tana mai gyara mata kwanciyar ta, Tace mata,, mama zaki sha ruwa ne, kai ta girgiza mata, YUSUF ya mike kamar wanda zai fita waje, daya daga cikin multinan da suka zo dashi yadauko guda dama yana da dan sanyi ya hado da gwangwanin peak milk guda naruwa daga cikin kayan da suka zo dasu wanda kusan rabin yan gidan suna can tsaye daga gefe guda ana kidaya yawan abin da aka kawo, Cikin dakin yadawi dauke da gwangwani mult da na peak, Inda maryam take yadan kalla batare da yadaga idon shi garetaba ya ce, Miko min cup mai kyau da spoon, Maryam ta hau dan dube dube cikin dakin ko,zata samu wani cup ko kwano mai dan dama dama, Wani kwanon sha na silver tagani can duk yadan yi kura shita dauko, Gyalen da ke jikin ta ta cire, ta aje saman katifar da mama take kwance sama, Da sauri tafita zuwa waje don daurayo kwanon Sai yau, hannun shi taba jikin Maryam wanda yaji kamar ya taba kada, Da kyat ya samu ya juye drinks din cikin kwanon sha A hankali ya dago kanshi yakalli inda maryam takw tsaye sam ta manta cewa bata da gyale a jikin ta ,,, Da sauri ya kauda idon shi gare ta saboda wani irin abu da idon shi ya hango, Anya, Maryam ce kuwa ko dai idon shi ne ya hasko mai ita, Yarinyar da yasani yar karama da ita, bata da komai yau ita ce ta koma haka, kamar irin yan matan hausawar da yake gani ana nuno photos din su a social median, Ki bata tasha mu gani kafin mu san abin yi, daga fadar haka ya mike tsaye yana kokarin kama hannun Assalam dan su tafi, Sun kasa kai kofar fita gidan yaji muryan maryam wacce bai masan cewa tana bi ye a bayan su ba, Nagode sai anjiman ku, Assalam ku gaida Anty sai na dawo ko, Takarasa zancen cikin muryan tausayi, Wani irin tausayi yarinyar taba shi dubawa yanayin gidan yakara yi sai kawai yasa kai suka tafi, Ita kuma ta juya takoma zuwa cikin gida inda ahaifiyar ta take kwance, Ko wanan karon shi da kanshi ke jan motar komawa kwantagora sai gudu yake shararawa daga shi sai yan yaran guda biyu, aciki, Tunane fam a zuciyar shi da tausayi ace mutum na irin wanan rayuwar ta talauci kawai zalla batare da wani damuwa ba, Hannu yasa ya shafo sumar kan shi dake masa kwance ya wani furzar da iska, yadaki sitiyarin motar, YUSUF ne a gaban Anty Dije wace ke mamakin jin cewa wai sunji kamfanin Bobi da kan su, Sun kai maryam wai har sun dawo ga kuma yadda hankalin Yusuf ya tashi na yadda yaga halin da mahaifiyar maryam taje ciki, Inda itama anty Dije nan da nan hankalinta ya tashi so sai , sai,matar ta bata tausayi, Duk wanan labarin da Yusuf kewa anty Dije bai fada mata irin dawainiyar77 da yakai, masu ba, Ranañ haka na ya wuni suku,ku baida wani ku,zari a jikin shi, Jibrin ne ya iso garin saboda yasamu labarin cewa Yusuf yana garin kwantagora, Da shirin shi ya shigo gari don zuwa ganin iyayen, Safiya, da yake son yi don a tsaida maganar si, A,kofar gidan su jibrin suke tsaye sai ga Aisha, tare da, Amina, Cikin wani irin shiga ba classic babies, abin har ya,wuce musali, Kallo daya yai mata, yaji koda tsayuwa da ita wani zub da mutunci ne a gare don haka ya, tamke fuskan shi, Cikin yar shagawaba Aisha ke cewa haba Joe ai bata karasa ba taji cikin wani irin murya yana ce mata Don't ever nerve call me with that name again Are out of your sense da zaki dan gan tani da wanan sunan a halin yanzu, Duk wanda ke gurin a cikin mamaki suke kallon Yusuf wanda ke ta faman fada akan kiranshi da Joe, Direct gurin motar shi ya nufa yana kokarin shiga don ya wuce, Bakaramin kunya da nauyi Aisha taji ba saidai abinka da wanda ya bushe fitilar shi , Tsaye tayi tana yar dariya cikin nuna kulawa, kamar bada ita yai wanan disgawan ba, Iam sorry na riga da na saba da kira hakane amna zanyi kokari in dai, na, Jibrin ne ya samu yadan kwantar wa Yusuf da hankali wurin kokarin jan shi da wani hira, Duk sallon yaudara da iya yi saida Aisha suka samu abinda suke so agurin Yusuf, Kuma ya mai data gida, da kanshi duk da bawai hira sukeyi da juna ba, Ita dai gurin ta dama mutane suce mata babban yarinya tunda har takai hurda da Yusuf, Maryam tana shiga gida ta tsaya da mamaki tana karewa Kayan dake zube a kofar, dakin mahaifiyar ta, Muryan mijin maman taji ya na ce cewa kai maryam ban san bakin da zanyi godiya akai ba wallahi, Kusan kwana, biyu nan duk yan dabaru mukeyi wallahi saboda duk dan abin dake gare ni jinyar mahaifiyar ki ya cinye shi, Murmushin yake tayi kamar gaske amma sai malam din yaci gaba da fadin A cikin kwantagora yake dan gidan waye shi halan da wanan da wai,niyar haka, Baba wallahi ban san gidan su gidan mu kawai yake zuwa Zancen ta baisa sun yarda da ita ba sun dauka wai kunya take ji, Shiyasa bazata iya fada masu gaskiyan zancen ba saboda nauyi, Dakin mama ta fada bayan ta gaishe ta sai kuma ta fara kokarin ganin ta gyara dakin ko banza su shaki iska mai dadi ai, Duk wani abinda yakamata tayiwa dakin tayi cikin dan lokaci guda ta kwashe kayan wanki daniyar zuwa tasai ruwa ta wanke, Kudin da Baba ya bata ta shiga mota da wanda, Anty dije ta bata don tasamu na dawo wa, Dashi tai niyar sayen ruwan, jawo jakar dazatayi ta dauko kudi , Sai ganin kudi tayi zasu kai kimanin dubu hamsin a jakar ta, Wani iri taji a cikin zuciyar tta duk inda tashin hankali yake hankalin maryam ya wuce nan, Da gagawa ta mike zuwa inda wayar ta yake a cikin jakar ta yar pos, Anty takara tambayar maryam lafiya jikin mama,inda take cewa maryam Ashe su Yusuf ne suka kaiki, har kamfani maryam daga rakiya tasha sai kawai ace antafi har bobi, Ànty cikin wata murya mai kama data kuka tace, kin san ko may Yusuf yakawo masu kuwa anty ? Yakai masu maryam shi Yusuf din ? Nan maryam ta shiga zayyano mata duk irin a binda yakai,masu Saiku tadan sasauta muryan ta kamar ta marada tace, Yanzu nazo zanyi wanki nasamu wasu kudi masu yawa acikin jaka ta anty, Shiru nadan wani lokaci anty Dije ta dauka tana tunane sai tace Yusuf ne nasan yasa maki su aciki don yasan cewa bazaki karba ba, To Anty ni may zai sa ya kashe kanshi haka wallahi ni bban son takurawa mutum sam, Haba Maryam yakamata fa sce kin san kowaye Yusuf zuwa yanzu, Bai kamata ki dinga irin wa yan nan maganganun ba dan Allah Wanan bawan Allah duk wani damuwa namu yana kokarin nuna concern din shi akai, Shiru Maryam tayi tana sauraron Anty dake magana cikin bacin rai, Rai a,bace Anty Dijen taci gaba dayiwa maryam fada Kara na biyu da Anty Dije takira sunan maryam again tace abinda nake so dake shine ki buga masa ki mai godiya, Nima idan ya shigo cin abincin dare zan mashi nawa godiyar, Sai tai magana cikin tausa murya tace, Maryam Yusuf mutum ne mai son taimakawa na kasa dashi ko yaushe, Baki ga yadda yazo tana nunamun damuwar shi akan matsalar rashin kai ta asibitin da ba,ayi ba, Wani irin sanyi maryam taji a ranta na cewa yadamu so sai da uwar ta, Yanzu kinsan yadda zakiyi kudin nan dan Allah kiyi kokari ki diba kiwa mama amfani dasu yadda ya kamata kinji, A sanyaye Maryam tace wa Anty Dije to na gode Anty, Amma duka kudin saidai in rago maki wani abu daga ciki ko,tafa ciki wata irin murya mai ban tausayi, Subbahanallahi maryam muda yakewa alheri ko yaushe muna ci, Sai dan wanan da yaiwa mama zan sa rai kuma haba dai, A sanyayae takara fadin to anty zanyi yadda kikace din, Kafin sukashe wayar Anty takara jaddada wa Maryam takira Yusuf taimai godiya dan Allah, Kayan wanki take hadawa amma tunanen yadda zata kira layin Yusuf da anty ta turo mata, takeyi, Aikin ta tacigaba dayi inda yan kannen ta maza da mama tahaifa a wanan gidan ke taya ta, Har zuwa dare takasa aiwatar da abinda aka umuce ta tayi, Gashi kuma Anty tace mata don Allah dai takira tayi godiya, Ita kuma bata son a hadata da Allah tayi abu taki yin sa, Saida tagama komai har yar fitilar kwan dake makale a dakin mama yau tasamu wanki ta kuma sa ancika shi da kallanzur, Yau mama tadan ji dama don har ta dan dago daga kwanciyae da takeyi kullun, Abincin da kishiryar ta tayi ne aka dan zubo mata awani plate na silver Ta danci shi sosai don har tana, yar lasar miyar dake a kwano duk da bataci wani abu mai yawa ba, Wayan ta tadauko, tafar lalubar nobar Yusuf da aka turo mata, Yusuf yana tsaye a dakin shi na hotel shi kadai bayan fitar Jibrin wanda, suka gama shirin yadda zasu tafi gidan su, Safiya gobe, Wanka yafito a lokacin yana dauke da wani dan farin towel a wuyan shi, Karar kira ce tashigo mai, alokacin saidai bakuwar noba ce yagani Kamar ya aje saidai kuma wata zuciya tace mai, Amsa kawai kaji kowaye a wanan lokacin da duk wani mahaluki ke bukatar hutu, Cikin yar siririyar muryan ta tayi mashi sallama, Saibkuma tai shiru wayar yadan daga yagani ko ankashe ne ,,, Amma sai yaji muryan muryan nacewa dazu kun dawo lafiya, Nagode kwarai Allah ya saka da alheri Allah ya bar zumunci, sosai Dama anty ce tace in bugo ma in maka godiya abin da kayi muna dazu din, Murmushin da maganar ta yasa shiyi yasa tace nagode sai anjima, Sai kawai ta kashe wayar nata batare da jiran taji ko da abinda zai ce, Wayan nashi yakara dagawa sai ya wurgata saman gado yaci faba da taje gashin shi da yakeyi, Sai mamakin zancen yarinyar yake yi nacewa anty ce tace taimai godiya, Wata ajiyar zuciya ta sauke gami da fesar da wata iska irin ta relief din nan, Bakin katifan da mahaifiyar ta take kwance ta zauna sai wani bala,in tausanyi ta yakama ta, A hankali takai hannun ta asaman wuyar mahaifiyar nata sai taji da zafi, har yanzu, Shin kodai malaria ne ya kama ta haka, ba wani kula, balle a yi treating, Gawani ruwan kwata kusa da kofar dakunan su daje fitowa daga wani lungun gidan, A zuciyar maryam tace gaskiya insha Allah gobe zan gwada gyara wanan gurin mugani ko zai rage aje ruwa haka, Tana kojarin kwanciya sai taji wayar ta na kara, mamakin may kiranta a wanan lokacin tayi, Don azaton ta ko A,A masugan ta ne yakira ta, nobar Safiyace Zagi tafara jefa mata da iskanci yanzun ne lokacin kiran mutum, Darita safiyan tayi tace ke dan Allah niki saurara koda yake ma nasan kin sani kawai dai zan fada maki ne dan karkice ban fada maki da baki na ba, Gobe Jibrin yace zasu zo su gana da mahaifina, kafin ya koma Wani irin dadi maryam taji, taitawa safiya din ba,a dakuma fatan alheri Safiya tace amma dai zaki shigo gobe din ko,maryam,? Maryam tace bani ma cikin gari safiya ina nan gurin mamana bata da lafiya, Safiya tace cikin mamaki maryam mama bata da lafiya shine baki fada min ba, A haka dai suka yi sallama bayan sun dan taba hira,a tsakani, Tana aje wayar sai zancen A, A yafado mata wanda tun jiya takirashi taje sheda mai abin da baba yaxo ya fada masu gamay da maman ta, Sauguda yakirata da safe yana tambayar ta koza ta dawo yau ne , Azaton ta ko zai ce zai tafine saitaji yace idan bazata dawo ba sai ya sani don kada yazo ace bata nan, Tsuki tayi wanda har sai da mahaifiyar ta cikin dakusasshen muryan ta irin na marasa lafiya tace, Baki ji dadin kwanci saman tabar ma ko yar baba,? Sai alokacin matasan cewa idon ta biyu zafin ciwo ne kawai yasa ta yin shiru da lafewa, Maryam tace mata aa mama mantuwa ne dai kawai nayi, Daga haka har dan barci yadan kwashe ta tana maicike da jin haushin A,A wanda tarasa ko wace irin soyayya ce yake gwada mata,,,,, Washe gari duk zancen boyar Allah da yagani acikin wahala ya cika mai zuciyar shi sosai, don da zancen ta ya kwana, Sai karfe hudu na marance zasu tafi ganin iyayyen safiya, Don haka, ya yanke shawaran cewa gara ya koma ya taimakawa matar yasa suzo asibiti adibata, Maryam tana tsakar gidan saye da wani tsohon zanin mahaifiyar tasai aikin gyaran kwatan sukeyi tunda sanyin safiyar nan Wani yaro yashigo yake cewa kishiyar mama wai wani mai mota yanawa, baba sallama a waje, Kafin tabada amsa sai gashi yafito yana cewa guri nako aka aiko ka mai motafa kace, Fitar shi ba,afi minti gomaba saiga su tare da Yusuf sun shigo, Yana saye da wata bakar rigar sanyi a jikin mai kama da leda bayan shi, yasa wandon Jean's, Mamaki ko rudewa yasa maryam tai saurin sake tsintsiyar dake hannun ta, Tana kallon shi cikin mamaki, Muyan mijin mamane ke kiran ta daga inda take tana wanke kafar ta, Cikin sauri da ladabi ta isa dakin kara gaida Yusuf din tayi tana mai tambayar lafiyan su antyn ta, Mijin mama yace maryama, asibiti za,akai mahaifiyar ki yanzu, Don haka sai ki yi kokari kishiryata kada mu makara ko,? Da mamaki ta waiga inda yake zaune kamar jiya, don har yau kujerar tana gurin, Wani yaro ya shigo dauke da wani ckofin silver mai marfi,da kosai acikin leda yace wai ance ga kunin ki, inji mamana, Karba tayi tace kace angode,ko kaji, Cup din kunun ta aje agaban Yusuf tace ga kunu da kosai, Sai ko taga ya aje wayan shi ya jawo kofin , sosai yasha kunun, yaraga mata saura, Yana gamawa yatashi zuwa waje, don ya jirasu su shir ya, ZEEE. MAKAWA [3/7, 1:15 PM] ‪+234 803 381 3188‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, A dadafe aka tallabo mama zuwa bakin mota,inda za a sata su tafi, Cikin sauri Yusuf, ya bude kofar motocin da taimakon shi aka tallabata akasa ta, acikin motar sai maida numfashi takeyi guda guda, Duk yadda, zaka zata matar na jin jiki fiye da hakan saboda duk ta zube, Maryam da ke tsaye gefe rike da wani leda da suka dauko ta dan kwantar da kai zabban tausayi, Saida yaga cewa an zaunar da ita, a hankali cikin motar sannan ya dan dago kai ya kalle ta, Fusksnta duk ya canza yana yi saita baka tausayi Kwana guda a kauye duk ta jemay tayi wani irin fau, da ita, Badake za,a tafi bane don bamu san ya abin zai kasance ba a can, Tajuyo ta dan kalle shi alamar kamar zatai kuka, alokacin, Cikin rawar murya tace, bari su tafi zan shigo motar haya yanzu in samay ku, A raunane yace no, bari dai abawa namiji kudin mota ya samay ko,. Don mata biyu da maza har uku ne suka matsa suka shige a wanan dirkekiyar Jeep din, Wacce tunda aka saye ta bata taba daukar loadi irin haka ba sai yau, Da sauri karamin yace shipa gaskiya ba zai sauka ba don dai dashi za,a tafi, Karamin ne yace ba matsala barin sauka, maryam da duk wanda ke cikin motar basu so hakan ba, Saboda Awalu yana da kokari sosai don kusan komai shike zuwa nemowa , Ya na sauko Yusuf ya ciro kudi dubu biyar cur yace ka shigo mota kasamay mu a asibitin tagwai pls, Ai ba kunya kuma sai Isah yayan shi da yace ba zai sauka ba, Yai caraf yace a,a shima motar kasuwa zai shiga ya fasa bin su, Wata mata tace amma dai kaikan ,Isah anyi mutumin kawai, Baka ji kunya ba, yace kedai kikaji dan nace kawai na fasa nima, Dariya suka sa alokaci guda duk wanda ke gurin, shiko isah ko a jikin shi, Shima dubu biyar aka bashi kudin motar kamar yadda akaba Awalu, Hakan yasa su samun fili su wala yadda suke so batare da sun matse ba, Baya maryam ta zauna tare da sauran matan dake baya, Yusuf ya tada motar shi inda suka fara tafiya sauran mutane na ta masu fatan adawi lafiya, A,hankali yake tuka motar cikin gwanin ta da kwarewa, Babata wani lokaci suka isa, cikin gari direct asibitin suka nufa, Sai da yafara fita yaga likita ba bata lokaci saiga wasu nurse da keken daukar mutane suka kama mama suka wuce ciki da ita, Suna shiga Maryam bata tsaya ba saboda duk a rude take a lokacin, Mashin ta hau sai unguwar su ganin ta kawai anty tayi, a lokacin, Da mamaki anty ke kallon ta saidai kafin tai magana tagane cewa maryam a cikin tashin hankali take, Dan natsuwa ta tattaro guri guda sanan tafara bawa anty bayanin zuwan su da kuma yadda suka kwana da maman jiya, Ita ma Anty Dije nan da nan ta rude ta hau shiru don su tafi, Saida suka fara zuwa gurin baba suka sheda mai tukun , Sannan suka wuce zuwa asibitin, ba tare da bata lokaci ba, Sun samu an daura mata ruwa, ana mata kari, Amma tana barci a lokacin don haka suka dan fito daga waje don gudun kar su ta da ita daga barci, Ganin yadda suke a tsa,tsaye tasa anty Dije shawaran zuwa gida don dauko masu, tabarma da dan sauran abin bukata, Tare suka fito ita da maryam a lokacin tanawa maryam fada cewa ta kwantar da hankalin ta dibi yadda ta koma jiya zuwa yau, Motar Jibrin ce agaba sai ta Yusuf din, nabin shi a baya, Ganin su yasa Anty Dije tsayawa don su gaisa taimai godiya, Both suka ga an bude tabarmi ne har da su filo sabbi yasayo masu sai kuma dangin kayan abin ci da sha,, Baki bude Anty Dije ke kallon shi cikin mamaki da abin da idon ta yaganar mata, Fa murmushi ya karaso gurin dauke da kaya a hannun shi wanda karasowar tashi tai daidai isar maryam kusa tana mai mika hannuwar ta takarba, Maryam tana barin gurin Anty Dije tace Yusuf waban irin dawainiyar haka, ? Saida yadan goge hannuwar shi da kyale, tukun sanan ya na murmushi yace, Anty wanan ne kawai irin damar da mutun ke samu ya taimakawa mabukaci, wallahi, Idan ba anan nazo naga mutane acikin yanayi ba a ina zan gansu a can tunda ba shiga cikin mutane mukeyi irin haka ba, Tausayi so,sai, maganar shi taba Anty Dije wace sai faman kada kai tajeyi don gamsuwa da zancen shi, Tace to amma dai ai zaka fada min kaga sai in dauko nawa agida ko, basai kasawo ba, Yadaga hannun shi guda guda na acikin aljihun shi yacewa anty dije, Haba dai No, no no, ai ya zama wahala hakan kawai a siyu yafi sauki, Ajiyan zuciya kawai ta samu yi tana mamakin halin rayuwa irin na wanan bawan Allah, Maryam ce ta karaso gurin tana rungumay da hannayen ta saidai fuskanta acikin damuwa yake, Alokacin Yusuf kecewa Anty Dije likita yace malaria ne ke damun ta so,sai shine sukuma wai sun cire mata hakin wuya, Ido daga anty har maryam suka fitar don mamaki jin maganar, Yadan kara gyara tsauwar shi ya na fuskantar su duk su biyun yace, Wallahi Anty mutanen mu na kauye suna kashe kan su da bata, Shiyasa bature ke cewa African people killed themselves by risks, before there, time, Kawai sun tashi kashe tane da lokacal treatment fa, Tun jiya dana ganeta hankalina bai kwanta ba,sam, wallahi, Yakare zancen yana dan siririyar, dariya ba mai tsawo ba, Kai, kai kauye dai gaskiya akwai jahilci sosai wallahi, Maryam tace cikin siriyar murya, Yanzu mai likita yace akai ? Dan kallon gefen da take ya yi sai yaji duk yarinyar takara bashi tausayi, Saboda duk yadda mahaifiyar ka take kana son abin ka, Yace nop likita da wai zai bamu magani akoma ai treating din ta a gida, Sai nace mai a,a yabarta kawai a nan mugani ko zata dan kara covering, zuwa gobe sai mu koma Ya kalli inda anty dije take tana gyara goyon Abubakar yace ina ga haka zai fi da ace su,koma gida a haka, O, O YUSUF mun gode kwarai wallahi Allah dai ya saka ma da alherin sa Haba, haba anty ki bari dan Allah wanan ai ba komai bane dai, Maryam ce ta hango mijin maman ta zai je bidan ruwa ya kewaya, wa, Da sauri maryam tanufi gurin inda taga ya dauki wani tsohon buta, takarba taje samo mai ruwan, Ido, suka bita dashi gaba dayan su yarinyar tana basu tausayi duk da tana kokarin danne damuwar ta, Shi ya maida Anty Dije gida don taje, ta yi girki, kafin yara,su dawo saboda bakowa gida, A hanyar shi ta dawowa ne ya ratse ya sai masu ruwan GOJE WATER, mai yawa da sabuwar buta, Da nama gassasa mai yawa tare da drinks, sai su fruit kala,kala, Maryam wace ke zaune saman steps din da zaka hau ka shiga cikin asibitin, Tadan yi tagumi da hannu ta biyu ba,abin da takeyi sai tunanen halin da mahaifiyar ta take ciki, Ga talauci ga wahala, ga kuma ciwo yazo ya shigeta haka lokaci guda, Badon Allah ya gyara ba da kilama surasata, ta wanan ciwon Maryam bata ga lokacin da ya iso ba don tati nisa a tunanen da takeyi, Saidai ganin mutum da tayi a gaban ta wanan karon yati wanka ya cire kanan kayan da yasa a jikin shi, Sannu da dawo wa ta ce mai cikin , karamar murya mai nuna damuwa, Ledar dake dauke a hannunshi ta mike tana kokarin karba daidai lokacin da mijin mama ya fito daga cikin asibiti hannun shi dauke da tasbaha, Ko bata bude ba kamshin da ya daki hanncin ta ya sanar mata cewa gassan nama na cikin ledar, Gurin da masu jiya suke zaune ta nufa da ledar, duk sukayo mata caaaa da ido Don suga komay aka dauko a cikin ledojin da ya shigo da su, Tunda tafara budewa sai da gaban ta ya fadi don ganin yawan abubuwan da yakawo masu, Shim shi wani irin mutum ne wanda baida jin zafin kashe ma wani kudi, Sun dade cikin dakin da aka kwantar da mama tare da likita da mijin maman, Dole haka tasa kai ta shiga don ta kai mata fruit din da nama kozata ci, Mijin mama ne yake cewa maryama cikin tausayawa, ina ganin fa yau duk baki ci komai ba, fa, Murmushin yake tadan yi tace na karya a gida ai kafin mu fito da,safe, Zai kara magana sai wayar ta dake a cikin yar jakar ta tai kara, A,A dun tane yakira duk da akwai mutane a dakin amma sai tadan daure tace hlo, daga haka tai hanyar fita waje, Ba gaisuwa ko wani abu sai cewa yayi a gadaran ce ya mai jikin, Da sauki tace mai a hankali, gamu nan asibitin tagwai, da ita, Tun yaushe kuke nan ya tambaya cikin dan nuna concern din shi, Tace mai yau da safe ne aka kawo ta saboda jikin nata ya kiya, Ok to zan shigo idan na rarage abinda nakeyi, Allah ya sauwaka daga haka ya kashe wayar shi kawai, Sam ta mantacewa a kusa da kofar dakin ta tsaya tana kashe wayan tadago kai sai caraf idon ta akan na Yusuf wanda ke kokarin,bude wani ledan magani, don aba mama, Jibrin ma wanan karon a cikin shiga ta mutunci shima ya shigo dakin yana mai gaida mama, Muryan Yusuf ne ke sallamar su yana cewa zasu dan je wani guri su dawo, Maganar Safiya ce ya fado mata arai azuciyar ta tace lalaima can zasu tafi ke nan gurin ganawa da mahaifan safiya din, Sai kusan bayan la,asar sosai A,A yazo asibiti cikin shigar shirt sky colour, da wando baki sai tie da yasa a wuyan shi kawai, Maganar shi a gadarance yake yin shi yana mai nuna cewa shi din wani ne, Tambayar mujin mama takeyi yasukabar har ciwo ya ci ta haka gasu ba wani nisa suke dashi ba da gari, Yace ai yanzu ba,a wasa da ciwo komai kan,kantar shi, Sai mijin mama yace to ko muna son zuwa asubiti da may zamu zo, Ko yanzu aida taimakon Alhajin nan ne muka samu mukazo in bashi ba ai da saidai yadda Allah yayi kawai, Kagashi nan da nan yagane cewa sai munzo asibiti ba na gida bane yanzuma gashi tasamu sauki, Da har zamu koma sai shi Alhajin tace mu bari har gobe sai ta dan kara samun sauki,, Lokacin jin tana ta cewa Alhaji Alhaji yasa shi waigawa gurin maryam wace ke dan rakube a gefen bango, Yace waye yake magana halan sai cewa maryam tayi a hankali, Yusuf ne, yakawo ta, Nanata sunan yayi yace Yusuf, Wani Yusuf ke nan, wai halan, ? Tace mai Yusuf wanda ya musulunta mana, maizuwa gidan mu, Ok Joseph ? Kai kawai ta gyada mai alamar eh, Mijin mama yace a,a a daba musulumi bane shi din,? AA yace kafiri ne yazo ya musulun ta koda yake har yanzu bawai an yarda da musuluntar nashi ba ne ai, Sai a lokacin maryam tadaga kai ta kalle shi saboda kalamin da ya fadi, Sai mijin mama yace a,a kai ko may za,aiwa shakka aciki tunda dai yariga ya musulunta, Mikewa yayi tsaye da kyau daga rankwafawar da yayi saman karfen gadon da mama take a kwance, Yace Arne fa ko ya mysulunta ai ba abin yarda bane, Jin kalamai da yakewa Yusuf ne sai taji kawai bataji dadin su ba sam, Don haka sai, tadan duka ta dauko wani leda tana kokarin fita daga dakin Ina zaki tsata mu tafi don gida nake son zuwa indan watsa ruwa wallahi duk nagaji, A tare suka fita daga dakin inda ta takai mai zuwa gurin motar shi, A nan suka dan tsaya suna hira a gagauce saboda ita ranan gata nan dai ne kawai, Shigowar motar suce tare da su jibrin da wasu abokan shi yasa su duka kallon inda suka tsaida motocin su,. Dakin suka shige gaba dayan su don su diba maijiki, A,A bai kara wani lokaci ba ya ja motarshi yabar gurin tare da Alkawarin zai dawo ya kara diba ta, Ba ai wani dadewa ba su jibrin suka fito amma ba da, Yusuf ba, Tana son taje dakin amma, sai tana jiran su fito saboda duk mazane acikin dakin, Kan ta na saman ciyar ta, ta dan duka tana tunane, Bakomai take tunawa ba sai mutumin ta watau A,A Wai shi wani irin mutum ne, hakana, ta kasa fahintar shi har yanzu, Gashi a fuska zakace ai baida matsala, sam, Kafin ta karasa sai jin muryan mijin mama tayi yana cewa, Maryam aida kinzo ya sauke ki gida ki dan huta tunda gamu nan da yawa ai, Kamar tace a barta kawai sai taga musu da babba baida dadi, Kuma ko banza tana da bukatar son watsa ruwa ajikinta, don tadan ji sanyi, Tafe suke su biyu a motar, a hankali yake tuki don marance ya fara abin hawa sunyi yawa a hanyoyin, Wani irin sanyi AC da kamshi ya gauraye motar, sai Qira,an dake tashi na Ahmed Suleiman kano, Kamar daga sama taji muryan shi yana cewa, Kiyiwa saurayin ki magana yadaina kirana da tubabbe pls, Batare da ya kalleta ba yake magana, zaka zata mako bada ita yake magana ba, Da,sauri Maryam, ta dan dube shi tankar zatai magana sai kuma ta fasa kawai tai shiru,,, Idan kasa zai tsage zata shiga don kunya wanan maganar, Wai ma ta ya ya ji wanan zancen, da akayi,, don dai baya nan a,lokacin, A rau,nane ya, yace ban san may guy din nan ke ji dani ba wallahi, Maryam dai har zuwa yanzu kala batace mai ba, Sai dai jin da tayi, ya furzar da iska har sautin shi ya iso inda take, Sai,dai,dai kofar gidan su,ya tsaya da motar shi, a yadda tagani duk rayuwar shi ya baci matuka, Dan Allah kayi hakkuri ban san lokacin da ya fada ba, Shima bai yi mata magana ba saidai ko karin Parker motar da yake yi,, A hankali ta bude, kofar batare da kara kalon inda yake ba,, ZEEE MAKAWA,,, [3/12, 10:47 PM] ‪+234 813 139 5577‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,, Assalamu Alaikum yan uwa musulmai tare da fatan kuna liya, Da plsn girman Allah yan uwa marubuta da makaranta kubani, dan hankalin ku dan pls Wallahi muji tsoron Allah musan cewa wata rana zamu gammu a gaban shi, In yanzu in anjima in gobe, Anytime kwanan mu yakare, Wallahi littafan batsa sunyi yawa yanzu sai mun kula mun gyara kada barna yai wa a sanadin rubutun mu,,, Amma idan maganata akwai laifi aciki ku yafe min pls,,,,👏👏👏👏👏 Alhamdullahi washegari mama tasamu sauki sosai don haka ta samu sallama daga likita amma zata dawo bayan kwana hudu, Sam Yusuf bai nuna gajiyar shi ba sai ma kokarin nuna tankar shi dan gida ne cikin su, Duk da bawai magana mai tsawo yake yi da su sosai ba amma zuwa yanzu sun dan fahinci halin shi, Idan ka gan shi zaka dauka wulakanci ne sai ka dan zauna dashi zaka gane miskilanci ne, Baban su maryam ne ya umarci Anty Dije da ta bar maryam ta, tafi ta kula da mahaifiyar ta tunda suna hutu, yanzu, Don haka maryam wace, suke wasan boya da Yusuf tun jiya da ce tafadawa saurayin ta yafita harkan shi, Sun isa kamfanin Bobi ana, shirin yin sallah azahar , Sai fitar su a cikin motar ne maryam taga, ashe duk kayan nan da yasaiya masu na amfani a asibiti suk sun kwaso abinsu sun zo da shi gida, Sosai ta jin,jina mai saboda bakaramin namijin kokari yayi ba gurin ceto mata mahaifiya daga halaka Da sauri maryam tashiga don ta gyara dakin mahaifiyar nata, inda sauran matan gidan ke ta mata sannu ya jiki, Saidai may turus maryam taja ta tsaya saboda ganin wani irin dindimay,may katifa sabo fil a cikin ledar shi, Da mamaki takarasa gurin inda daya dafa cikin matan ke sheda mata cewa, ai daga can kwantagora akazo da shi ance na mamantace, Ga sabon randar roba ta ruwa, ga kujerun roba farare guda uku, da filolin su, Jiki ba kwari zuciya fam da tunane maryam ke aikin dakin, Ko ba, a tambaya ba tasan cewa aikin Yusuf din ne haka, Kafin wani lokaci dakin mama yakoma kamar wata yar birni, can, Sai zuwa dare maryam ta samu dan hutu bayan ta tabbatar cewa mahaifiyar ta tadan yi,wanka tasha magani, Washegari da safe maryam na idar da sallah, asuba bata zauna ba fitowa tayi don taimakawa kishiyar mama da wasu aiyuka, Saida ta tabbatar tagama komai ta koma daki don ta taimakawa mahaifiyar ta, Kafin gari ya karasa haske duk maryam ta kammala komai a nata fan,nin, Matan kauyen sai shigowa sukeyi da sunan gaida mama da jiki, Amma azahiri gulma ke kawo su don wasu basu ko iya boye gulman su sai su dinga latsa katifa ko taba wani abu ace irin na wance na wance ne,,,,, A, dadafe yafito daga cikin motar shi da taimakon Samuel yasamu yau yafito zuwa shagon, Inda yakan zauna can nisa kadan saman kujera yadinga kallon masu harkokin su a cikin gari, Wani dan kabilar su saman wata mashin ta matasa yazo ahan mai, Ganin Mr Ema a gurin yasa shi zuwa gaida shi har inda yake, Anan bayan sun gaisai sunyi ya kwana biyu ya jiki mutumin ke tambayar shi cewa a she, Joe yana gari ne, ? Da mamaki yakara tambaya yana mai kada kai da kafar shi yana rage haushin da maganar ta rasta mai acikin zuciyar shi, Inda mutumin ke tambayan shi cewa ko suna da mara lafiya ne a asibitin tagwai, ? Wani sabon mamaki ne ya kara kamashi inda yake cewa, w Watau Joseph yana nan yana yiwa hausawa da yaran su dawai niya ke nan, Zaune yake idan kagane shi a lokacin zaka dauka cewa, cikin jin dadi yake Amma sam cikin tashin hankali yake inda yanzu yasha alwashin cewa, sai ya koyawa Joseph hankali tukun, Akwai wasu samari yaran hausawa yan wi,wi yan daba su yayi haya, Inda ya fada masu abin da yake da bukata su yi mashi akan Yusuf, Shiko Yusuf yana can a unguwar Rimaye ystafi kaiwa wani malami dake unguwar sadaka, Wanda zai tallafawa almajiran shi da su a gina masu babban daki inda zasu dinga kwana, Malam Shehu mai almajirai na Rimaye yai mamaki kwarai da wanan alherin da Allah ya basu cikin lokaci guda, Addau,a na muhinmin yasa ai mashi cikin, dafifin almajirai inda yabisu da sadakan yan hamsin, Sai wani makarantar matan aure da ke Kan Wuri, bayan sectaria inda yakai masu sadakan abin zama tare da kara masu girman makarantar, Wanan abin ya jawo magana sosai duk da duk inda yakai alheri sai yace dan Allah kada a fadi a saya shi domin Allah yayi, Amma ina mutane saboda mamakin irin halaiyar shi sai an fada cewa da ace sauran masu kudin mu zasuyi koyi da shi da sun taimaka wa al,umman musulai, da basu dashi, Daga hotel din ya ke yana sauri saboda yana son zuwa gurin wani mutum da zasu yi hurdan ,Noma a shekarar bana, Wasu matasa ne a saman mashin guda uku, suka biyu shi, Dafari bai kula da cewa shi suke bi ba saidaga baya ya hankalta da su, Sannu,sannu ya fahinci cewa shi suke bi, a baya a hankali yasa signal, ya tsaya gurin wani katon iccen mangaro, Security guard din shi ya kunna nan da na signal yakai gurin security din shi da koyaushe a cikin shiri suke suna biye dashi, Kafin yafito yaji saukar sanda a bayan motar shi duk da hankalin shi ya tashi amma sam bai nuna masu tsoro ba, Muyan matasan yan daban yayi suna cewa kai karamin dan isaka wa zai yarda da musuluntar ka, Har yanzu mu kafiri kake a gurin mu. Don bamuga ka iya sallah ba tukun ko sabbi saukan mata baka iya ba,,,,,, Wasu bakaken motoci ne wulk guda biyu suka gani shake da security cikin bakaken kaya suka tun karo su, Da gudu suke kokarin haye mashin din dasukayo haya don su gudu,, Cikin rashin sa,a sai guda yafadi kafin yai wani yunkuri aka cafke shi, Nan da nan gurin ya cika da jama,a makil, mutane da son ganin gulma, Shiko dan matashin sai cewa yakeyi Dan Allah kuyi hakkuri ba nikadai bane turo mu Ema mai manja yayi muyi mashi haka wai yai mashi laifi, Yusuf najin haka ran shi ya baci sosai bai tsaya ba sai kawai ya shiga motar shi A fusace ya isa gidan nasu tun daga wahe yake kwaka wa mahaifin shi kira, Wanda shiko Ema yana can yana fada da samarin nan yace may yasa suka bishi a cikin gari, Jin yadda Yusuf ke kiranshi yasa shi katse wayar don jin abin da yazo da shi, Yana zaune falin shi saye da wata yar babban ringar banga ta lace, baka, kanshi saye hular su ta yan kabilar IBO, Dad if you want to killed me killed me by yourself pls, Amma kada ka sa kanka cikin harkan yan daba yaran da basu san komai ba sai kudi, Su jawo maka magana kawai Idan da suna da wayo da wallahi bazasu karbi aikin ka ba akaina, Gaskiya baba wanan abin da ka aikata yabani mamaki, Dad idan kaso pls kayi hakkuri da musulunta na dan ba zan taba komawa cikin kuba don kuma muna maku fatan dawowa hanya mafi alheri, Daga haka yasa kai yabar gidan cikin bacin rai, da kunar zuciya, Direct police station, yanufa don yasa a sake yaran don shi sam baiga lai,fin su ba, Duk yadda police sukaso a dau,kaka karan bai,yardan masu ba saboda yasan cewa mahaifinshi zai wulakanta akanshi, Duk abinda ake ciki Mr Ema nada labarin komai saboda yan leken asirin da yasa tabaya, Tun da yabar police station din yaji kawai ya ma rasa inda zai nufa, Kai tsaye ya kama hanya sai kamfanin Bobi, inda ya shiga garin bayan la,asar lokacin har maryam sun gama girkin abincin dare ko, Cikin mutunci mutanen suke gaishe shi tare da nuna kulawar su da jin dadin su, Sai godiya suke mashi akan irin taimakon da yaiwa mama, Wani dan dadttijo yace yaro mungode kaji, Allah ya hada hankulan da diyagga kaji, Sam bai fahici manufar su ba saboda hausan shi bai,kai can ba, Tare da kanin mijin mama suka shigo cikin gidan shi yai mashi iso, Harzuwa dakin mama Alhamdullahi don yau mama,azaune take saman tabarman roba da maryam ta shimfida, mata, a can gefen dakin ta, Kai tsaye inda take zaune suka nufa inda Awalu ke mata sheri yana cewa a,a,a yaukan sauki yasamu kece zaune a waje, Yusuf yana kokarin zama yana gaushe ta yana kuma yi mata ya jiki, A cikin gwari,gwarin hausar shi yake ma mama ya jikin yakuma take ji yanzu, Sai a lokacin maryam ta iso gurin shi cikin sakin fuska taje mai sannu da zuwa, dakuma ya hanya, A hankali bayan ya furta mata cewa lafiya ya jikin mama sai take ce mai ya su Assalam da Issalam, Saida yai murmushi sanan yake cewa, gaskiya yau bai samu zuwa gidan su ba, Amma dai sunyi waya da Anty Dije da safe, kafin ya fito, Yauce rana ta farko da wani magana mai dan tsawo ya taba shiga tsakanin su, Maryam na kokarin mikewa ne taji muryan mama tana cewa ke yar baba ki ki bashi abinci a daki, A razane maryam ta dago kanta don tasan cewa, bazai ci ba, Amma sai taji baice komai komai alamar zaici, Muryan Awalu ne ke cewa, haba yaushe Alhaji zai iya cin ,abincin mu, Maryam ta fahinci zai ci don haka bata kara cewa komai ba ta hada mai a saman tire takai mai dakin mama inda ta dan fito, Sai cike take da jin kunya kalar abincin nasu da zai gani, Tuwon dawa ne da miyar danyen karkashi sai, naman kassa na rago da aka zuba, aciki, irin local miya akayi shi bawai da stew daban ba, Ruwa ta debo mai a,randar kasa mai sanyi cikin kwanon sha, A hankali taji muryan shi kamar mai rada ya na,cewa,, ki dan taimaka min Maryam da ruwan wanke hannu pls, Ruwan tadebo,ta,mai a,cikin wani silver mai fadi, Sautin murmushin shi taji yana cewa, Awalu yatafi ni kadai zan zauna a dakin, Babu shiri maryam ta koma, can gefen katifa, ta zauna tana dan wasa da yatsun hannun ta, Daga inda take zaune tana ganin yadda yake cin abincin hankali kwance, yana mai lunshe ido, Shikam ashe akwai wanan irin abincin har yanzu anayi, Rabon shi da irin wanan tun suna yara da yake bin su KB da jibri gidan kakan nin su, suna ci, Saidai daga ita har shi ba mai ma wani magana, shidao kokari yakeyi da farko, yaci kada mama suce yana kyamar su, sai kuma koyi da sunnah dayaji ance yana da kyau, Amma sai gashi ya buge da ci sosai fiye da tsanmanin shi, Saida ya kusa gamawa yadago kai yakalle ta inda take zaune a takure,yace, May sunan wanan abincin,? A hankali tace tuwon dawa miyar karkashi, Yana mai tsamay hannuwar shi zuwa cikin ruwan wanke hannu yace, Dazan dinga samun shi akoda yaushe da bazan ci wani abinci ba sai shi, Kanta ta gyada almar mamaki, jin maganar shi,da yayi ita da take ganin ba zai iya ciba, sai ga shi ya buge ga santi, Yunkurin mikewa tayi ta kwashe kwanonin agaban shi, Amma sai taga ya ciro kudi masu yawa ya aza saman ture din yace pls kiba matan gidan nan su raba, Muryan ta na rawa tace, kai haba abin ya,yi wa gaskiya, Kamar ba shi take ba don sai ma kokarin goge hannuwanshi da yakeyi, A, hankali ya fara kokarin mikewa zuwa bakin kofan dazai fita,daga dakin, Ya juya da kyau ya fuskan ce ta yace aikin Alheri bai yawa ga inda ake bukatar yi, Ba rokona sukayi ba can,cantar hakan naga yadace nayi, Idan nabar wanan taki bazan kara zama free man ba sai lokacin dana dawo kuma, Cikin nuna kariya tace mai Allah ya saka da alheri Allah yasawa saura albarka, A, a maryam albarkan iyaye nake bukata ba ta kuba yaran zamani, Kala maryam batace mai ba don kada maganar su yai nisa sosai, Da sauri ya nufi hanyar fita waje tun kafin ta gama hada kayan abincin, Kowa agidan sai murnan kudin da ya raba musu su keyi dubu guda guda kamar a mafarki, Wasu daga cikin sun ne ke cewa maryam gaskiya kin yi dace, Da mamaki maryam ke tambayar zuciyar ta kamar ya ta dace, Caraf ta ce masu nifa ba komai a tsakanin mu dashi gaskiya, Sam basu yarda ba sai zolayar ta sukeyi, suna mata ba,a Maganganu barkatai suka dinga yi akai kowa na fadar albakar bakin shi, Sosai lafiya yasamu ga mama wace yanzu take iya yiwa kanta wasu abubuwa, Mama da maryam ce acikin dakin suna yar hira ta sakanin uwa da , "yar ta, Yar baba may ke a tsakanin ki da wanan bawan Allah ne wai,? Cikin wani irin kallon mamaki maryam ke kallon mahaifiyar ta, Mama tace duk da naga alamar ba wai kina son shi ba ne Ki daure ki kalli kyawawan dabi,un shi kiyi nazari akai, Maryam takai wani,,, lokaci tana jimamayn zancen mama azuciyar ta, Washegari sai gasu shida KB da Jibrin da Assalam Sai kayan fruit niki,nike da sukazo dashi daga can kwantagora,, Ranan Dan wake su maryam sukayi da mai da yaji, sai kunun gumba yaji kayan yaji yana ta kamshi,y Sosai sukaci wananyaci jiyw, danwaken gaba dayan su har shi Assalam din nan yusuf ke masu hiran irin abincin da ya ci jiya da yazo, ZEEE MAKAWA [3/12, 10:47 PM] ‪+234 813 139 5577‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣6⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,, Yan uwa har wayau ina mai kara maku tuni akan barnan da wasun mu ke kokarin yadawa acikin al,uma, Baidace abin da ke boye mu fito fili kara muna yada shi ba fa, Musa jin tsoron ubangijin mu da mairubutawa da mai karantawa, Allah yasa mu gane gaskiya,👏👏👏 Zaune yake a office din shi dake a cikin Abuja, inda yanzu yafi bada karfin zaman shi, Gaban shi tarin takardune yake dubuwa sai gefe guda inda system din shi yake a bude dagani aiki yake acikin sa, Baka jin komai sai karan na,urorin sanyin da ke office din suna ta aikin su, Sosai hankalin shi ke ga wasu takardu da yake diba inda yake nazarin su, Kokari yakeyi ya kara haffako da arzikin masana,artar shi da Sonny yabar mai shikadai yanzu, Duk da Sonny din ba,wai yabar masa abanza bane, don abi biyu zuwa uku yabar mashi, Na farko dai, yasan cewa sun samu riba sosai da gurin cikin dan kankanin lokaci, Sai kuma kokarin da yakeyi na yabar duk wata harkan business din shi a Nigeria, kwatakwata, saboda rayuwan shi a yanzu a can take don iyayyen shi sun mutu, Nabiyu kuma yanzu Yusuf ya zama musulmi irin wanda ba guda ba jada baya, hurda dashi zai mashi wuya don yana gudun yazo ya jefashi a cikin kamar yadda shi ya shiga, Na uku yana tausayin abokin shi Joseph acewan shi don yadda yaga yan church suna ta faman bugo mashi waya akan ya cire shi a harkan shi, Wanan abin yasa yaga cewa Yusuf ya cancanci yabar mai wanan gurin amatsayin tukwicin zaman da sukayi suna business a tare da dadewa, A hankali ya dan juya da kujerar da yake zaune yana mai nazarin, takardan da ke hannun shi, A hankali ya cire glass din dake idon shi ya kara kurawa takardun ido, har zuwa dan wani lokaci, Bakomai bane sai takardan wani business din motoci ne da suka sawa hannu da dadewa kuma gashi har lokacin business din ya yi, Sai,dai matsala guda gashi basu tare da Sonny yanzu don haka bai san ya abin zaici gaba ba, Don dai harkan ba karamin alheri zata jawo masu samu so,sai , Bai bata lokaci ba gurin kiran Sonny don ya tunar dashi akan zancen business din da zuwa yanzu komai ya kammala ko, Kira guda ga nabiyu Sonny din yadaga wayar yana mai cewa A,loo, Nan dai suka gaisai da junar su suna mai, ya kwana biyu ya aiyuka, A tsanake Yusuf yai,wa Sonny bayanin komai kamar yadda da farko suka tsara, Kafin Yusuf yacigaba da bayani Sonny ya katse shi yana mai ce mai, to ai yanzu wanan business din yadawo nashi shi kadai Cikin mamaki Yusuf ke sauraren bayanin Sonny din don hali irin nashi sai antona Abinda shi Yusuf bai sani ba shi ne, yanzu Sonny yafi karfin wanan karamin business din, Don ya na harka da masu hada kwaoyoyi mahaukatar kudi nazo mashi ta ko ina har bai san ya zai yi da su ba Allah ne yafitar da Yusuf daga ciin wanan har kan kafin abin yai kauri, Har sunan shi ya shiga cikin bata gari , A je wayar yayi cike da mamakin halarcin da Sonny yai mai a rauyawa, Hannu yadaga sama yai,wa Allah godiyar irin wanan baiwa da yai mai a,cikin lokaci guda, Ga baiwar samun haske na shiga cikin addinin musulunci dayayi, Ga kuma ta samun cigabar arziki da yayi acikkn lokaci guda ta yadda bai taba zaton arzikin shi zai kai haka ba, Wanan samun cigaban yasa Yusuf daukar ma,akata da dama daga kasan kwantagora, saboda cigaban su, Har mai Sudan saida yasa akakira mashi Yusuf yakara yi mai godiyar irin taimakon da bawa kasan shi tare da taimakawa matasa,,, Maman Choima yanzu sun dawo abuja tare da Ejoma wace idan baka sani ba zakace blood sister din Yusuf ne ita, Saboda yadda take taimaka ka mai tsakani da Allah ga al,amarorin shi, Ejoma ta dade a cikin zuciyar ta tana son ta zama musulma kamar yadda tun tana yarinya take da ra,ayin haka, Saidai batai dace da musulumin kwarai wanda zai tsaya akanta yaga cewa ta musulunta, Sai ma baya da yajuya mata don kada ya sha wahala, akanta, Kwance take rub da ciki saman gadon ta,dake dan karan dakin nata na cikin gida Anty ta, Tana saye da wani dogon riga baki mai yar hannun shimi, har kasa rigar tie ce ta mastse ta ta tsakiya inda tadan cire top din rigar ta aje saman kujerar ta, Dakin yasha gyara dan har wani kyali ties din kasan dakin keyi gawani kamshi dake ta shi , Takardun ta ke nazari tana kuma dan rubuto a gefe guda, daga kwancen, Wayar ta, touching kiran ardriod tana gefe guda saman gadon sai waka ke tashi, Wankan Fadar bege, inda yake wakarshi mai take, Sarki Jiran Halittu, mijin juwairah, Tanayi tana dan maming din wakar daga kwance, Issalam ce ta shigo dakin da gudun ta tana rataye da jakar makarantar ta a baya, Sai kokarin cire takalman ta takeyi kuma tana kallon kofar shigowa gida tana dariya, Maryam sam bata kai hankalin ta ga abinda yarinyar ke yi ba, Sallama yakara yi cikin kwantar da harshe kamar a mafarki taji muryan, nashi, Don dai baji Anty ta na zancen zowan shi ba kamar yadda ta saba yi,indan zai zo, Dammm gaba ta yabayae wanda batasan dalilin faduwar gaban ba , A hankali ta sauko daga saman gadon cikin sanda, tana mai karba sallaman, Sam ta manta cewa yar rigace a jikin ta saida taga ya kauda kai yana mai komawa baya, Tai saurin komawa cikin dakin tadauko hijab din ta tayafa, Zaune yake a saman kujera yana mai dafe da kan shi da hannu guda alamar gajiya, atare dashi ga kuma su Assalam nata faman mashi surutu, Sannu da zuwa ta iya furtawa ta wuce wurin da fridge yake dan dauko mai ruwa, Tai mamaki kwarai dataga cewa ya,shaye duk gora guda na ruwan da ta aje mai don ko cup bai dauka ba, A kunyace maryam ta gaishe shi, Inda ya karba mata ba wani sakin fuska kamar kullun, Ta juya zata wuce don kiran anty a wayan ta, don ta,tafi gurin barka a makwabta, Kamar daga sama taji yakira sunan ta, a wani murya na kasalance, A tsorace maryam ta juyo, sai yanzu ta kula da kalar kayan jikin shi, Wani yadine na maza fari mai taushi kamar lece, Sai kyalin fari yadin keyi har yana kashe ido, Saidai duk da tadan ta takure dan zaman motar da yadan yi, Kanta ta maryam kasa don jin abinda zaice mata, saboda bazata iya jure kallon shi,,, Muryan shi taji yana cewa ya jikin mama hope taji sauki sosai, Tana wasa da yatsun hannunta ta hada su wani cikin wani Tace taji sauki sosai yanzu Alhamdullah, ba,a magane cewa tayi ciwo ai, Masha Allah yace, Tana kokarin barin gurin kuma sai taji yana cewa, ga keys pls a shigo ma anty da kaya ciki, Kayan tsarabane sosai kamar yadda yasaba kawowa yazo da su, Manja, Irish, sai Doya gudan mai yawa, Almajirai tasa suka kwaso zuwa cikin gidan su inda Anty Dije ta samay su akofa gida tsaye tana sallamar yaran, Tare suka shigo inda Anty take mai, korafin rashi sanar da ita, zuwan shi, Kayan da tagani yasa tai tsai da maganar ta, takasa karasawa, Wai kai Yusuf baka gajiya da dawainiya haka kulun, Kai ya langabar kamar yaro karami yace ana gajiya da yiwa dan uwa dawainiya ne Anty, ? Taji dadin maganar shi har cikin ranta sosai, don yadda yake nuna cewa shi nadu kamar yadda minin Anty yai mai nasiha bayan musuluntar shi, Dacewa yadauke su tankar jini guda don yin haja zai sa yarage wa zuciyar shi radadi, Sanan kuma mutum bai zama baida yan uwa aduniya Don haka yazama yana sake jikin shi dasu har zuwa lokacin da yan uwanshi zasu huce dashi, Abinci suke kokarin gabatar mashi amma sai ya, dakatar da su dace bazai iyaci ba don yana jin ciwon kai a halin yanzu Daga Anty har maryam a lokaci guda suka waigo shi Maryam wace sai, yanzu ta lura da cewa tun da yashigo yake dafe gishin shi wanda ita tadauka ba komai bane, May ke da,muwar ka Yusuf, ? Lafiya kalau nafito amma sai naji kawai na kusa shigowa Minna kai,na yai,wani sarawa, Sannu suka dinga mai gaba dayan su har yaran yana amsawa a hankali, Masaukin shi ya nufa don yaje ya dan watsa ruwa ya huta,. Amma sai yaji kan nashi kamar yana karuwa ne, Ibrahim yakira don tare suka zo dashi cikin sauri ya,samay shi, Saidai yadda ya samay shi din ya bashi tsoro sosai don wani irin yake ji, a kan nashi, Ga wasu jijiyoyin sun fito mai rada, rada a lokaci guda saman goshin shi, Ibrahim yakira mahaifin shi, ya sanar dashi abinda ke faruwa, Ba bata lokaci Abdulsamad ya iso masaukin na Yusuf inda kallo guda yai mai yafahinci ko may ye, Sosai rashin lafiya Yusuf yake cigaba, a dan kan kanin lokaci, Asibiti suka tafi cikin daren nan, don yadda yaje ji tankar kan shi zai tsage a lokaci guda, Bayan yan "yan tambayoyi da likita yai mashi sai kuma su ka bashi magani da,sauran yan shawarwari, Kamar kar su dawo masaukin shi abin sai kuma yafi da karfi, Sai wani kugi yakeyi, yana tallabar kan shi ko kuma ha dinga bugawa kamar zai fasa, Wayar shi ce tai kara don haka Ibrahim ya dauka dan ganin mai kiran don yasan cewa ba zai iya daga wayan ba, shi Yusuf din, Anty Dije yaga anrubuta,,, Muryan wani taji yadauka alokacin da take kokarin yi mashi sallama, Ji tayi yana cew sorry mai yawan baya da lafiya saboda sanin dayayi kowaye anty dije ga Yusuf, Cikin rudewa take ce wa subbahanallah, tambayar shi ta yi cewa yana ina, yanzu,? Nan dai Ibrahim ya sheda mata gidan da Yusuf ke sauka a wani Lolo, Ested, dake GRA, A motar kanin Illiya costume suka zo gaba, dayan su, Maryam wace ke dauke da Abubakar a kafadar ta ta, da kuma wani basket, Cikin rudewa anty dije ke fadar umm,uhmm subbahanallah, Wanan wani irin ciwo ne haka, acikin dan lokaci guda, Gaskiya wanan ciwon yakamata a san abin yi akai bawai abarshi a haka ba Don dare ake ma gudu, kada abin yafi nan worse, ko ya kukagani, Ibrahim yace ai yaga mahaifinshi yace yana zuwa yafita, Bai fi minti biyu ba da fadar haka sai ga malm, Abdulsamad da mahaifin Jibrin sun shigo, Tundafa nesa mahaifin Jibrin ke cewa subbahanallah a,a,a Wani malami suka shigo dashi dan matashi ba wai wani babbba ba, Tun bai taba Yusuf ba yace akwai matsala fa aciki, Rukiya yai mashi sai,gashi yai wani irin atishawa mai karfi, A, hankali yafara mai,da numfashin shi, guda guda daga haka sai barci yadan dauke shi, Su Anty sunkai wani lokaci a tsatsaye suna kallon ikon Allah, Saida dare yadan yi malam Abdulsamad yace ai su tafi gida har zuwa safe, su dawo, Tunda zuwa yanzu yasamu barci insha Allah komai zai zo da sauki ai, Duk kan su jiki ba wani kuzari suka iso gida zuciyar su fam da tambayoyi, A lokaci guda yakoma wani dan feyau, dashi duk ya zube yawani je may , Kwance yake yawani dunkule guri guda, kamar jariri, aciki, Mafarki yayi da wasu na binshi da wasu irin makamai masu cutar wa, Da gudu suka biyu shi sai da zo gaban wani mutum mai wasu kaya shudi,shudi sai tsaya inda ke binshi a baya baya, Kamar zai fadi sai ce La ilaha illah ant subbaha nika in,ni kun,tu minal zalimin, Da karfi ya furta a fili yazabura ya mike zaune, wani iri yaji akan shi lokaci guda, Zaune ya mike tana mai dafe kan shi sai wani zufa yake yi,kamar yana acikin ovon, Addu,oi sosai suka dinga mai har zuwa rukiyar da karatun alkur,ani mai tsarki, Barcin da yasamu wanan karon yadan yi nauyi so sai fiye dana farko, Washegari tunda safe anty ta hada mai abin kari a cikin basket, Amma sai maryam tace ai masa kunun kamu da kosai, don wata,kila zaifi son su da ruwan tea din,, Ita kadai anty tabawa abin karin nashi takai don ita, babu motar da,zai zo da ita,yanzu, Sai da gari yawaye ya haska sosai yasamu farkawa daga barcin, Inda yai yar madifar rashim tashe shi da ba,ayi ba da guri har gari ya waye haka, Zaune yake ya takure wuri daya can kuryan daki Dai,dai kwanar wani dan standing drower dake a cikin dakin, Falo ta tsaya ta aje kayan sai kuma ta ja tai saye guri guda, Tana kallon Ibrahim wanda ke kokarin aje kayan saman dan dining table din da,ke dakin, Ibrahim ne daga inda yake tsaye yake mata magana cewa, ta shiga aiyana nan zaune, A nutse ta rika takawa har zuwa cikin dakin,inda yake, Duk da baida lafiya sanyin A, C ne ya gauraye dakin, sai kamshim turaren shi da yake yawan shafawa akai a kai, watau turaren THE,,, Babu kowa a dakin sai shi kadai, Jin sallamar Maryam yasa shi dago kai a hankali, ya kalle ta, yana mai ansa mata sallamar ta,,, Ban garen da yake zaune a takure idon shi a lumshe, Yabude su a hankali ya sauke su ida tak ke tsaye a bakin kofa Maryam ta kalla, shi sai, taji wan irin tausayin shi ya kamata lokaci guda, A marairaice kamar mai shirin kuka maryam tace ina kwana, Uncle Kamar yadda taji su Assalam naki ranshi da sunar, Tace mai ina kwana ya jikin, Kanshi yadago yakalle ta saida taji gaban ta ya fadi don yadda idon shi sukayi wani irin ja, A hankali kamar mai jin zafin furta magana ya ansa mata da cewa lafiya Maryam, Ya anty da yaran suke, wani iri taji lokacin dayake maganar don dagani yana jin jikin shi so sai,saidai daurewa da yakeyi irin ta maza,,,, ZEEEE. ,MAKAWA [3/12, 10:47 PM] ‪+234 813 139 5577‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Rubutun novel tankar wani fadakawa ne ga al,uma, Duk novel dole akwai sakon da yake isar wa zuwaga al,uman,hausawa da musulmai, baki daya, Don haka mu fahintar da matasan mu alheri a ko yau,she ba mu koya masu yadda rayuwa zata gurbace ba,, Allah yasa mu dace baki dayan mu Allahuma Ameen 👏👏👏👏👏 Maryam takai wani lokaci tsaya daga inda take, A hankali tace mai cikin sanyi murya mara sautin furtawa Ga abin karyawa nan a falo, nakawo ma,, Anty tace ya jikin naka? Saida yadan gyara zaman shi yakara dan dunkulewa guri daya, sanan Ya dago jajayen idon shi da suka rine sukai mai ja jajir kamar garwashi, Gabantane yakara ba da dam sai ji tayi tankar ba Yusuf wanda ta sani bane take kallo a lokacin, A hankali Maryam ta isa har kusa dashi, kai kasa cike da jin nauyi Maryam, tace mai kasa hannun ka a goshin ka kadinga karanta, Falaq da Nas da Iklas,, kowani uku, uku, katofa, a hannu, kashafe kan ka da shi, Har zuwa jikin ka, sai,ka kara karantawa a cup kasa a ruwa, tare da Ayatul,qursiyyu, Sai kuma a samu wanda zai karanta ma suratul,Jinn, gaba dayan,ta Duk gankali shi ya tattara yake sauraron ta, don jin bayanin da take mai, Tana kai nan tace mai Allah yasa mu dace Allah ya bada sauki, Ibrahim wanda ke tsaya tun fara,zancen ya ce ma ogan shi ya kawo mai abin karyawa ne, a falon, aka aje, Da kyat ya iya dan girgiza mai kai, a,alamar a,a, Marayam tace mai a kwai kunu da kosai a ciki da ta damo mai, A hankali yace wa Ibrahim yakawo mai kunun kawai bada kosai ba, Ya,dan yunkura a hankali ya zauna da kyau, Dan karamin kofi ne amma sai ya kasa shanyewa duk, Da sauri maryam ta fita zuwa falon sai gata dauke da cup da goran ruwa, A hankali ta dan durkusa gefen shi ta balle goran ruwan ta tsiya,ya ruwan kusan rabin cup din, Ta kai cup din daidai bakin ta tafara jero mai addau,oi acikin ruwan, Tsawon yan mintoci tana tofe ruwan dasu har zuwa inda takai aya takara dan tofawa, Mika mashi cup din tayi tace ya sha yadan shafa saura, Ido takafa mai har saida taga ya shanye ruwan saura kadan sai tace wa Ibrahim ya shafa mai aduk jikin shi, Mikewa tayi a hankali da niyar barin kuryan dakin cikin mutuwar jiki, Ido ya,bita dashi don bai taba sanin tana dakirki ba haka sai yau dayaga ta tausayawa ciwon shi sosai, har da bashi addu,a, Muryan ta yaji tana cewa Ibrahim yai mai kamu a goshin shi , Daga haka tasa kai, zuwa waje, inda ta ke kokarin barin gidan don komawa, Babu wani sallama taji kawai tayi karo da mace, tana kokarin shigowa gidan, Aisha ce cikin wani dogon rigar dinkin material ja mai laushi, dinkin mai dogon hannu ya dane mata cas, Ganin Maryam yasa Aisha yi mata wani irin mugun kallo naje wace, Inda ta aje yar pos din ta da ta sa kudin mashin din ta tanufa, Ke, daga, ina kike haka,? May ya kawo ki,nan,? Zata kara magana sai ga Ibrahim ya budo labulen kofar yana cewa Maryam wai yace kice ai,mashi tuwon dawa ya ke so, Wani mugun kallon ke baki isa bada amsa ba Maryam ta watsawa, Aisha wace ke tsaye tana mamakin ina wanan tsaleliyar budurwan mai zubin fulani tafi nan, Jin muryan Maryam, yakara ruda ta a lokacin da taji Maryam nace wata irin miya za ai mai, Juyawa Ibrahim yayi zuwa cikin dakin yadan leko yace wa maryam wai ta shigo, Kusan a tare suka shiga dakin da Aisha wace ke wani irin shu,umin kamshi, duk gidan ya bure da shi, A kwance tasa mashi kasan dan karami carpet din dake tsakiyar dakin ya kifa kan shi a filo, Da kyat ya dan iya juyowa inda take yana ce mata, Ki min irin wanan miyar da kika taba yiwa mama a Bobi, Aisha wacce a lokacin har ta kara inda yake kwance tana kokarin zama, gefen shi gab da shi, Maryam ta kara watsa mata harara tasa kai abinta zuwa gida, Zuciyar ta fam da Allah waddai da irin halin rayuwa irin ta,su Aisha, Maryam na barin gidan Aisha ta waigo inda Ibrahim ke kokarin kawar da cups din da aka bata, Sai ce mai Aisha tayi wanan yarinyar yar gidan waye ita,? Yar gidan Anty ce Ibrahim yabata amsa a,takaice, Yusuf wanda tunda ta shigo bai,yi magana ba yace mai ya faru da kike tambaya, ? A hankali tana kokarin kai hannu gare shi don wai ta taba lafiyar jikin ta ji inda sanyi ko zafi, Cikin wani irin karfi ya hankade hannun nata tun kafin takarasa kaiwa a jikin shi, Cikin wani irin murya yace mata May ye haka pls, ? Murya irin ta mai shagwaba, tace, to ba zan ji inda zafi bane jikin naka, Tsuki ya ja yana mai juya kwanciyar shi ya kauda kan shi gefe guda, Idon ta yakai ka inda yar brief case din shi take a yashe can gefen gado a kasa, A hankali kuma takara daga ido tana mai karewa dakin kallon tsab, Shigowar yan dattijan biyu ya banna wa Aisha tsari a lokacin, Sam batai farinciki da shigar su a daidai wanan lokacin ba Dattijo Abdulsamad na ganin ta ya ran shi ya baci don baya ra,ayin irin yaran nan sam, masu zubar da mutuncin su, haka, Don yanayin shigar ta kawai ya ishi mutum yagane kowace iri ce ita don ba kunya a tare da ita sai fitsara Dole tabar dakin cikin fushi don ganin manya suzo, Gaisawa sukayi da shi cikin cijewa yake magana Don shi kadai yasan yadda yake ji a jikin shi lokacin, Sai wani zufa daya tarso mai daga jikin shi duk da sanyi A,C dake dakin, Sun tambaye yadda yake ji tanzu sai yake sheda masu yadda ya kwana, Sai kuma zuwan Maryam da taimai addua yashe sai yaji wani irin abu kamar a fisge mai wani abu daga cikin kun,nuwar shi, Yace saikuma wanda tace Ibrahim ya shafa mai ajikin shi Shi tun lokacin yake jin wanan zufan na tartso mashi, daga ko ina na jikin shi, Juna suka kalla suka kada kai, don jin maganar tashi, Mahaifin Jibrin yakalli kofa inda Aisha tabi yanzu zuwa waje yace, Ita wanan din dai da naga ta fita yanzu, tai maka addu,an, Ibrahim' da shi kan shi Yusuf sukace a,a a lokaci guda, Ibrahim ne ke fada masu cewa Maryam kaunar Anty Dijen shi inda yake zuwa cin abinci idan yazo, Yusuf din ne ya mike zaune a hankali yana maida numfashi guda guda gami da yin ajiyar zuciya, A, kamshin gaskiya wanan al,amari akwai jinnu a cikin shi, ko sihiri, Duk da halin da Yusuf ke ciki na jin jiki bai hana shi yin yar murmushi ba, Ya dan kalli inda suke yana mai yin murmushin karfin hali ya ce ciwo ne kawai dai zo min a haka, baba, Su ma dai murmushin sukai mai a lokacin don, sun san bai san komai ba, tukun daga sheri dan adam, Ibrahim ya kalle cikin yar karamar murya yace mai ya kuna mai hearter yai wanka, Da tai makon Ibrahim yasa mu ya mike zuwa cikin makewayi don ya dan watso ruwa ko zai ji sanyi a jikin shi, Ita,ko Aisha ganin cewa wa yan,nan yan dattawan biyu basu da niyar fitowa yasa ta cewa bari taje ta dawo idan sun wuce, Don ta sa rai acikin yar briefcase din nan nashi da tagani a yashe, Ibrahim ko yana ganin Yusuf ya shiga wanka shima sai ya hau gyaran dakin Inda ya kwashe sauran kaya yasa acikin wardrobe din bangon dake dakin, Ya kule ya tura keys din a cikin aljihun shi ya koma falo don ya karya, Sai a lokacin ya lura da cewa Aisha ta ta,fi kila don bai ganta ba, Har waje ya leka yagani ko zai ganta sai dai babu ita babu alamar ta ya ja yar guntuwar tsuki yakoma cikin don shi sam batai mai ba, Yusuf yafito yasamu babu kowa a dakin dan haka sai yadan zauna a bakin gado, Cikin shigar jallabiya yadan samu yafito falon shi yazauna, Remote din TV ya dauko ya kuna TV, inda ya kamo NTA kwantagora, Ya soma kallo, A inda yake a hankali ya soma jin kan shi na wani juyawa kamar za,a kife shi a gurin, Addu,an da ta koya mai ne yazo mai arai don haka yadan lumshe idon shi yana mai rike kan shi da hannu guda, Sannu a hankali yake yi yana tofawa a hannun shi ya shafawa asaman kan shi har bayan shi, Kamar an wallawale shi yaji saidai kuma yaji baya kaunar kallon TV don haka yabar shi a kunne ya koma ciki, Sallama take ta kwadawa babu kowa a falon hannu ta dauke da basket, din abinci, Sai TV da ke ta aiki shi kadai, a lokacin, babu kowa agurin Tai mamaki kwarai na rashin ganin wani a gurin a lokacin, Don haka sai tai shawaran ta diba dakin ko suna ciki, Babu kowa a dakin sai shi kadai, ke kwance saman gado, Idon shi a rufe tayi sallama ta shiga a tuna,nen ta ko barci yakeyi a lokacin, Don haka sai ta juya a hankali don ta koma falo ta aje basket din, Da wata dishashiyar murya yakira, sunan ta a hankali, Batare da ya bude idon shi ba dake a rufe, A, take jikin ta yai wani sanyi, Cikin dakiyar murya tace ai ina ce ko barci kakeyi, ta samu kanta da fadar haka, Shiru na dan wani lokaci bai sauke hannun shi da ya dafe goshin shi ba, Don haka sai tai niyar juyawa still don ta aje abincin dake a hannunta, Da sauri ya sauke hannu yakalle ta da rinanun idanun shi da sukayi jawur, sai kace wanda yai kuka, Da sauri maryam tace subbahanallah, Wanda fadar hakan yai daidai da shigowar Ibrahim wanda yaje dayan dakin yai wanka, Ibrahim yace mata cikin muryan damuwa,har kin dawo ko ? Ta amsa mashi da eh a takaice,, Muryan Yusuf sukaji yana cewa cikin lumshe ido dan Allah ki kara yi min addu,an dazu don naji dadin shi sosai wallahi, Basket din ta aje ta koma falo kamar dazu da dawo dauke da ruwa da cup, Wanan karon a bakin gadon da yake zaune ta zauna da kanta, Baiyi aune ba sai jin hannun ta yayi a saman goshin shin Sannu a hankali tafara rairo mashi addu,oi tare da wasu ayoyi masu koran shedan, A hankali ta zare hannu ta daga goshin na shi da ta rike, Wani irin, lunshe ido yayi lokacin da yaji ta zare hannun ta daga goshin shi, A cikin cup din take addau,a akaro na biyu indon ta a lumshi take rairo karatu, Daga shi har Ibrahim kallon ta sukeyi cikin mamakin jin yadda take rairo karatu, cikin murya mai dadi, Bayan tagama ta tofa sai ta mika mashi, tabash da kan ta ya karba yashan ye, Sai yadan rage saura kamar yadda tace dazun, ayi, ibrahim ne ya matso da sauri, yakarba ya sha,shafa mai ko ina, Har inda take taji yadda yake ajiyar zuciya, da karfi, Tsam ta mike tsaye daga zaune zuciyar ta duk a chakushe, , Saboda dagani ko ba,a fada ma ba kasan yana jin abu, so sai, Karan kara sauke ajiyar zuciya yayi tare da yin wani irn, atishawa, mai karfi, Shiru yabiyo dakin duk kan su uku ba mai cewa komai har zuwa wani dan lokaci, Kowa da abin da zuciyar shi ke sakawa, alokacin,, Sautin muryan shi taji yana cewa ta taimaka ta zuba mai abin ci Ba musu ta nufi gurin basket din nan,ta zuba mai leda guda na tuwon ta bude bai cikin place plate, Amma sai yace ta rage ahankali takai duban ta ga abinci wanda ko rabin plate bai yi ba, Dankadan ta zuba mai ya mike zaune da kyat, yana cije labe, Takwao ruwa tazoba mai sai ta aje mai wani plate don wake hannu, Kadan yaci yature plate din yace ya ko shi, Su hudu suka shigo wanan karon on tare da wani tsoho mai farin gemu taf ga fuska, Wanda sun shigo ba,a dade ba su KB da Jibrin suka shigo su ma wanda isowar su ke nan garin, Ibrahim yakara basu labarin duk abin da ya faru bayan fitar su Tsohon nan mai farin gashi yai yar murmushi irin ta manyan masana, Kallo guda tsihon yai mashi ya matsa kusa da Yusuf din ya kamo mai hannun shi ya rike acikin nashi ya mai furta wasu addu,oi, Sai ya sake hannuwar na Yusuf yakalli inda malm Abdulsamad yake yace, Yace wallahi sihirine mai karfi akan shi, irin wanda, duk wanda akai mawa shi sai Allah,kawai, Yace wasu kafiran aljannu aka hada shi dasu, don yaji cewa kasar kwantagora tafita a rayuwar shi kwata kwata, Abdullsamad yaka da kan shi yace nasan za,ai haka gaskiya shi yasa naki bari mukaishi asibiti kamar yadda aka bukata, akai shi din, Yace nasan halin mutanen mu basu barwa Allah abu sai in sun ga cewa abin yafi karfin su, Yace wallahi akwai wace aka haukata, mace, saboda kawai ta musulunta, yace mai makon yan uwa musulmai su dauketa ai mata magani ko Allah zai kawo mata sauki sai akabarta har ta mutu hakanan, Sai daga baya labari yazo min nan cewa ga irin abinda ya samay ta ai, Amma a,lokacin ni banda karfin da zan taimaka mata, har manya nadinga bi ina fada masu amma ba wanda ya kula, mun, Yace haka wata kuma itama mace ce wani abu suka turo mata agaba takoma wata iri duk inda taje sai kokarin tabudewa mutane suka gani taje yi, har ta kare a hakan, Balle irin kabilar mahaifin shi Yusuf din ko a cikin IBO tsiron su ake ji don mugun tsafin su, Shima ai an mashi mai kyau ke nan, tun da basu haukatashi ba, Mahaifin Jibrin yace ina fa mai kyau malam Abdulsamada a haka,? Allah dai ya haushe shi kan su kawai, zamu ce, yanzu kan dole ne mu tashi tsaye sosai gurin ganin mun yakince su, Dakuma badhi tsari madu karfi ajiki da addu,oi masu kariya daga sammu, Jakar da ya shigo da ita ya bude ya ciro wani shake ya mikawa, mahaifin jibirin din yace su shaka mai a fara gani, Sai,kuma yafida wani kulli acikin wani tsunma, ya,mika masu, yace a samo garwashi mai wuta, amai hayaki da shi, yau zuwa gobe gaba daya kafin ya dawo,,,,, ZEEE MAKAWA [3/12, 10:47 PM] ‪+234 813 139 5577‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, Har kulun kira ga marubuta yan uwa na musada alheri ga al,uma yafi sada shedanci ga al,uma, Bin ra,ayin wasu don farauta masu zuciya bashi zai taya ka zaman kabari, ba, Duk sakon da muka rubuta gobe sai an tambaye mu akan shi, Mutuwa ba fashi haka Hisabi ba fashin yin shin gobe kiyama, Tun a makwancin ka zaka gane makomar ka, Allah kaba ikon rubuta alheri a sakon nan mu, 👏👏👏👏👏👏👏 Tun da ya shaka shake yake wani irin atishawa mai karfi, babu kakautawa, Sai ya baka tausayi idon shi sun rine sunyi ja jajari kamar garwa shin wuta, Sai hayakin da tsohon ya bayar yace ai, mai shi gaba daya a ranan, Daga gidan Anty Dije akazo da gawayi wuta saboda basu san mutane su san cewa, Yusuf baida lafiya haka, har labari yakai wa mahaifin shi, Wanan malam tsoho din shi da kanshi yazo tare da wasu yaran shi, Duk wanda ke cikin dakin akace yafito waje ya samu guri kada ya tsaya kuma tsaye, Idan ma son samu ne dan Allah duk su watse subar malm Abdulsamad da , mahaifin Jibrin, Haka akayi kuwa don su KB da su jibrin da Ibrahim duk barin uguwar su kayi, gaba dayan su,, Fara karaun su malam bada wani nisa ba sai murya sukaji da yare ana magana, Malam tsoho yadaga kai ya kalli Abdulsamad don ya yi magana, A cikin harshen IBO suke ta gwalancin su da malam Abdulsamad din, Abinda suke cewa shi idan ba yabar kasar kwantagora ba bazasu bashi peace of mind ba zasu jagula mai lissafi, Yai ma malam tsoho bayanin abinda suka ce, sai kuma cewa da sukayi saida a ka yanka masu katuwar bajimin shanu suka sha jinin shi sunyi ma wanda yasa alkawarin cewa za su yi mai aikin shi kamar yadda ya kamata, Malam yaba yaran shi umurni suci gaba da karatun alkur,ani kawai, babu tsayawa, Wani irin ihu suka tsala saida wasu suka firigita murya sak na irin IBO din nan tipical one wa yanda basu da imani sam, Sai suraitai sukeyi da yaren su na IBO suna ta zun duma asharrr, Duk wanda ke tare da Yusuf hankalin shi ya tashi a lokacin don ganin irin yadda yadinga yi, Sun jima akan shi sosai sai daga bisani suka ji muryan su suna cewa sun bar shi har abada Duk da haka ba,a daina karatun ba saida sukaga cewa ya daina komai da yake dazun sanan su ka dakata, Kwana biyu suna sintiri akan shi tare da bashi addu,oin da zasu taimaka mashi, Sai yau da yaciki kwana biyu da samun sauki, Jibrin ya kwaso su Anty tare da Safiyar shi da maryam sukazo gaida Yusuf a gidan shi dake Abu,lolo,Eastern, Maryam da Anty da yaran su , suna bayan mota zaune inda Safiya ke zaune gaban mota tare da Jibrin, Iyakar burgewa sun burge Maryam sosai tun lokacin da Anty tace wa Safiya ta zaune gaba tare da Jibrin din, Saida suka tsaya wani shago sukayi mai tsaraban kayan fruits kala,kala shake a leda duk da Jibrin yace kada su saye, akwai shi cike a gidan, Amma sai Anty Dije ta, ce su dai saye tunda ba,a zuwa gaida mutum hannu saje, Zaune yake saman sallaya a folon shi ya kunna tashar madina yana sauraron kira,a, Yana saye cikin wata yar farar jallabiya mai guntun hannu, Da sallama suka shiga inda Ibrahim yatare su cikin mutumci, Ànty Dije tace a,a lalai Yusuf jiki yai kyau, tunda yau gaka zaune, Yana kokarin tashi zaune don tariyae su hannun shi yana dauke da casbaha, yana ja, Da murmushin maganar da anty tayi yakai zaune da kyau saidai bayan shi na jingine a kujeraa, Kafin ya kai karshen murmushi sai Anty Dije takara cewa gaskiya dai ya kamata yanzu ace Yusuf ka aje mata kodon taimaka maka da wani abu, Yar dariya mai sauti yakarati daidai lokacin da ya zauna da kyau Assalam yana kusa dashi zaune, Jibrin wanda ke shigowa adaidai lokacin yaji maganar da Anty taiwa Yusuf sai ya cabe zancen da cewa ai barshi kawai anty, Dama akwai wata Cousin sister dina da ta sani gaba da zancen Yusuf tunda dadewa, Ibrahim dake ta gurin fridge yana aje ledojin da suka shigo da su yace, Aiko zakayi fada da Aisha idan taji ka da wanan zancen, Kai Aishan may can inji Jibrin wanda ke kokarin zama saman kujerar da Yusuf ya jingina akai, Daidai lokacin yadago kai inda Safiya da Maryam suke zaune guda saman kujera guda tana zaune a hannun kujerar, Murmushi yai masu yana mai ansa gaisuwar da safiya tai mai, Itama maryam gaishe shi tayi a hankali tare da tambayar shi karfin jikin shi, Duk hiran da akeyi daga Maryam har safiya babu mai cewa komai daga cikin su, Sannan ita Maryam bata jinko mai gamay da Yusuf har kasan zuciyar ta, Kamar yadda shima Yusuf din bai, jin komai gamay da maryam azuciyar shi sam,. Dan daukar ta yajeyi a matsayin yan uwa kawai daga ita har Anty Dije, Daga kofar shigowa gidan suke jin murya ana sallama, Ibrahim ne ya leka dan ganin mai yin sallaman alokacin Baban su maryam ne da Anty wai yatafi gida ake cemai sun zo nan mai,gidan bai jin dadi shi ne, Duk sunyi mamakin ganin baba amma sai suka ga cewa kanin ya illiya ne ashe yakawo shi, Baba yai mai fatan alheri tare da fatan samun sauki, Anty Dije ce take cewa baba yau ba,a fita kasuwa ba ke nan ko ? Kaiyya Dije ai kasuwan sai a hankali yanzu, mutum ya fita tun safe karshe baifi yasamu abin sayen abincin rana ba kawai, Yanzu kinga aiduk dan jarin ya karae sai maneji nakeyi, kawai, Allah ma ya taimakeni nasamu makwaci mai albarka shike taimaka min watarana, Baba bai dade ba ya mike yana cewa to shi zai koma, inda su Assalam ke cewa baba tsoho ka sayo muna mangwaro a kasuwa, Maryam tace akin a saya maku nawa kuka bashi jari, Baba yace a,a yar Baba kyale su ai zan sayo masu ko kadan ne, Saidai ba kamar da ba leda ce ya miko wa Yusuf yace abin gyaran baki nagani a hanya nasiyo ma, Jibrin ne yamike yabi bayan baba da yara suka bishi har kofa suna cewa ya sayo masu abu kaza da kaza, Sai ga baba yadawo cikin mamaki da kudi rike a hqnnun shi yana gwadawa Anty dije kudin zaikai dubu biyar, Yadinga sa masu albarja dafatan alheri a rayuwan su, Sai da baba ya wuce Anty dije tacewa maryam ta dauko wa Yusuf fruit ya sha, Yadan daga kai yakalli anty yace da na anbarshi ai, don ban dafe da sha ba, Maryam wace a lokacin har ta dauko wani plate ko daga ciin basket din abincin da suka shigo da shi, A gaban shi ta aje fruit din har zata juya sai Anty tace mata, Bude ledar da baba yakawo mugani, ko may ye acikin shi haka, ? Zogala, ne mai yawa hade da kayan gyaran shi Wani plate ta,dauko ta juye aciki inda Anty, ta bukaci a zuba mata, Tayi hakane don Yusuf ya sake jiki yaci zogalar don zai gyara mai bakun shi, Har safiya saida suka vi zogalan amma banda maryam wace ke zaune ta kura ma tv ido tana kallon yadda ake rubuta haruffa kira,ar da akeyi, Ke baza kici ba ne, yatan baye ta a hankali saida safiya tadan tabo ta sannan tagane da ita yake yi, Kan ta dake kasa ta girgiza tana wasa da wani dan stone da ke makale a gefen kujera, Idon ta kem akan shi sai yanzu ta ga irin raman da yayi cikin kwana biyun nan, Harda wani dan kwarmi kwarmin gurin idanun shi yayi, A hankali yake cin zogalar shi hankali kwance ba abin da ya damay shi, Kallon shi sosai taba da himmar yi, hakan yai daidai da dago idon shi daya don yace ta miko mashi ruwa, Kanta ta mayar kasa da sauri, cike da jin kunyar shi na kama ta da yayi tana mai kallon kurulla, Maryam help me with water pls, Yace alokacin da ya kura mata ido, A kunyace ta ansa mashi da to, Tamike a hankali har zata fara tafiya sai kuma ta tsaya tadan kalli inda yake tace mai sanyi ko kuwa, Kai ya girgiza mata alamar a,a mara sanyi yake so, Goran ruwan majidadi water ta aje mai a gaban shi, ruwa mai kyau da tsabtar sha, Sai cup da ta hado mai dashi nan yaron anty Abubakar yaga ruwa sai yaron ya hau tsalen cewa abashi ruwan yasha shi ma, Yaron na,ta kokarin zillowa daga jikin uwar shi, Abubakar sadiq ko ruwan kake son shane inji Yusuf wanda hankalin shi ya kai ga yaron, Kyale shi kawai, a,a haba anty ruwa fa yake so, ko banza aikin san mai sunan ba abin wasa bane fa, Sunan amin ma,aikin manzon Allah ne, shiyasa nake girma ma duk mai wanan sunan, Ruwan ya tsiyaya a cup ya cewa Maryam miki min shi yasha, Yaron ke faman kwankwadar ruwan amma ita maryam duk wani irin shock ke jan ta, Saboda dan hucin numfashin Yusuf dake bugo ta, Shima bangaren Yusuf din hakane yake ji kamshin turaren Bushrah da black oud din data shafa duk ya wanu susuta shi, Zogalar da yadaina ci ke nan saboda wani irn mugun kasalar da ya sauka i a lokaci guda, Assalam ne ya cinye duk sauran zogalar Idon shi yana a lumshe bayan shi da wuyar shi suna jingine da kujera, Kamshin yakara dukan hancin shi abinda ya sanar mai da cewa maryam takara zuwa kusa dashi ke nan, Muryan tace tana ce mai ga ruwa ya wanke hannuwar shi, Thanks a lot ya furta a yar siririyar murya ta yadda ba kowa ne zai iya jin shi ba, Bayan ta yabi da kan lo nadan second sai yai sauri ya kauda kan shi dan guda shiga hakkin ido, Ita ko maryam tana shigowa falon daga gurin da taje zubar da ruwan Sai ce masu tayi tana mai kokarin daukar gyakenta anty mutafi ko,? Jibrin muke jira yadawo dafa sayen magani ai, ko, Dole ta koma ta zauna saman hannun kushin din again zaman da yai daidai da kiran wayar ta, Kamar kada ta dauka saidai ta daure ta ciro dan ganin kallon da Safiya tai mata, A,A ne kiran ta saidai kuma ta tsinci kanta da jin nauyin ansa kiran nashi, Har kiran ya katse bata dauka ba, tana kokarin mayarwa a jakanta ne wani sabon kiran yakara shigowa, Dole badon taso ba tadauka tana mai cewa Assalamu Alaikum, A hankali take ansa mai maganar sai kuma tamike tsam daidai lokacin da take cewa mun fitane zuwa unguwa, duk kan mu Idon kusan duk suka bita da, bishi a lokacin kowa da abinda yake sakawa a ranshi, Shiru yadan biyu baya a falon sai Yusuf ne ke, cewa Assalam gobe tare zamu tafi massalaci ko, Sai a lokacin Anty Dije wace ke wani tunane can ta dan nisa tana mai cewa, Har ka ji saukin fitane Yusuf aidade ka bari har ka, kara, ji sauki, ko,? A haba no,no,no Anty ai zan iya zuwa insha Allah I am ok now, Kaiwa a shirya min shi, mutafi, Zaune yake a gaban dan dan matashin dattijon yana taunan goro yace wallahi Ema ina fada maka cewa shi nagani a massalaci dazu, Mr Ema ya dan ce no,no,no nafadama bashi ba bashi ba, Joseph ba zai zo wanan gariba again Saboda idan yabar zuwa wanan garin, zai dai na sa addin ku a zushiyan shi, Amma waik,a she min kagani Joseph namu a mosque naku karya ne Isowar Edowed shi ya tsayar da zancen su da yare suke gaisawa bayan sun gama gaisawa ne Edowed ke ce mai ashe Joseph yazo ne, What, yafada da karfi har yana dan yi kamar zai mike tsaye sai kuma yakoma ya zauna saboda wani irin duhu da yake gani, Dauda wanzan nata cewa to Ema nikan zan shige ke nan sai wani lokaci ko? Kai douda idan zaka tofi ka wushe abunka mana may,nene ne kana damay ni haka,? Rana ko yar biyar bai samu ba gurin uhan gidan nashi da ko yaushe yakewa fadanci, Tsaye yake a gaban wani standing table dake dauke da kwalaben giya kala,kala, Magana yake makama da fada ko kuma rada,,kamar wanda bai,son aji may yake cewa Samuel wanda yai niyar fita cikin shirin shi nazuwa evening service, jin abinda mahaifin shi ke cewa yasa shi komawa baya yasha jinin jikin shi don sauraron uban, A hankali ya,koma baya, don gudun kada uban ya gan shi, Maganar uban ke mai yawo a kunnuwar shi, don may mahaifin su zai ma dan uwan shi haka, Bayan irin girmama shin da dan uwar nashi ke yi amma ce duk,mahaifin su bai gani ba, Saboda kawai ya canza addinin da yake bukata, don ra,ayin shi,,,,, Gaskiya bazai iya kyale wanan zancen ba zai fadawa brother din shi don yasan abin yi tun wuri, Yadauki wani ikacin don ya gwadawa uban cewa baiji komai ba, Da harara Mr Ema ya bishi don yau duk haushin kowa yake ji, Har yadan gwauta shi sai ya sa mashi kira yadawo baya, Kallo guda yai mai sai yaji duk mahaifin nasu yafita mai a rai, Tambayar shi yayi ina zai tafi sai yake cewa uban na shi zai tafi, service ne, Fuska murtuk yakada mai kai alamar yatafi, Saida Samuel yagama fada ma Yusuf duk abinda yaji uban na fadi ga waya, Yusuf ne cikin murmushi, yake kwantar wa da kanin shi Samuel hankali da cewa ba abinda zai samay shi insha Allah, Amma sai Samuel din cikin rudewa yake cewa no, brother you know how uncle Jackson is, That man can kill person "I swear, Samuel just cool down your mind, Dad will not do anything, successful to me, Da haka yai,ta kwantar wa Samuel da hankalin shi shi har ya yarda ZEEE. MAKAWA,,, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Sosai maryam ta maida hankalin ta ga karatun dake a gaban ta, Na ci gaban zango da,zasu shi badadewa ba saboda sani cewa FCE ba wasa ga al,amarin karatu a gare su, Cikin sauri sauri take tafiya,saboda kada, ta makara, Tsaye take a bakin titi tana jiran taxi yazo, sai motoci ke gittaiya a gaban ta, Wata civic ce da ta,wuce tayo ribas baya ,baya,zuwa inda take, kokarin tsaya wa motar take yi, Ganin haka yasa Maryam kau,da kan ta gefe, guda, kamar bata gan shi ba, A hankali ya sauke glass din motar shi yana mai mata wani kallo cikin natsuwa, Ina zaki haka ne, don na wuce dazun nan kadan naganki tsaye a nan, Sau guda ta kalle shi ta kau,da kai, saboda kwarjinin da yai mata a fuska, Murmushi yayi yace, well, Kiyi hakkuri in sauke ki pls kada ki makara, don ko baki fada ba nasan cewa, F C E zaki dan ganin yanayin shigar ki kawai ya nuna min haka ya karasa zancen shi yana mai daure fuska, Kai ta,daga ta dan kallan titi ko zata samu motar da zata shiga, Titin, kamar an, share ba taxi tafe a lokacin, don haka ta daure duk da zuciyar ta bai kwanta daganin mutumin ba, A hankali ta zagaya zuwa dayan gefen, na mai zaman banza, ta bude a hankali, ta zauna,. Nagode tace batare da ta kalli gefen shi ba, wakan dan kwairo ya na Sarkin Das Billiyaminu, Kidan, wakar na tashi kamar speaker din zai ruguje, abayan motar Sai sanyi A, C da yacika motar da kamshi air freshener da ya gauraye motar, Tsam Maryam take a cikin motar zaune kawai take amma kamar, jira takeyi, a ce mata ke ta sheka, Shi bai mata magana ba ita ma din dai batai mashi magana ba,. Daidai get din farko yadan waigo inda take, a karo, na biyu yai mata magana, Tun bayan shigar ta motar, tambayar ta, yake yi, Wani guri zai sauke ta a cikin compound din makarantar, Da musali har suka kai inda zata sauka motar ,sai a wanan lokacin maryam wace hankalin ta ya kwan,ta ganin cewa, sun shigo cikin mutane, Tace na gode Allah saka da alherin sa, Dai,dai yana ribas da motar, shi, ya dan waigo inda take yana cewa kai ba komai ai Iam Alhasan Bashir, daga zaria GTBank, manager, Saida maryam ta waiga saboda jin abinda yace, ina fatan hajiyar zata fada min, sunan ta, Maryam Abdullahi Bobi, Ta fadi a takaice batare da ta kalle shi ba "nice name yace, kawai A,lokacin da ya balle mata marfin motar ta fita, batare da kara kallin shi ba, Har yai nisa da motar ya yadan lumshe idon shi badon komai ba sai don shakar kamshi turen ta da yayi, a karo na biyu, Yana son mace mai yawan amfani da kamshi, Yanason mace kamila mai aji, Yana son mace wace bata canza halittan jikin ta, Dan ganin Maryam da yayi yau sai yaga cewa duk ta, tara, wa yan nan abu,buwan da yake bukata, Maryam Abdullahi bobi ya kara nanata sunan a hankali, Tsaye yake a bakin motar shi, hannun shi a cikin Aljihun wandon shi, Sam bata ganshi ba sai kokarin gyara saba jakar ta takeyi Jikin tane yabata cewa ana kallon ta sai kawai ta daga kan ta sama, gurin da tasan ana anje motoci, Ido biyu, sukayi da A,A dinta yana tsaye hannun shi guda, a cikin aljihun shi, Sai guda da ya rike kofar motarshi kafar shi na ta ciki kadan, Damm gaban Maryam ya ba da, amma sai ta dake kawai, A, tsanake take tafiyan ta batare da ta nuna mai wani darrr dan ganin shi ba kamar yadda takeyi da, Mamakin yakara kama shi kwarai don bai yi zaton haka ba daga gare ta, Tafiya yakeyi, amma hankalin shi na ga wanan guy din da yaga ya aje Maryam, Wayan ke ta kara batare da an dauka ba, har wayan ta katse, Wani sabon kira takara yi a karo na biyu, sai,dai ko rabi ba,ayi ba a ka daga wayar, Ke yar kauye ya kike inji Jibrin yaje cewa Sadiya Mohammed joda, Bayan sun zauna tare da yi wa juna barkwanci a tsakanin su, Sai Sadiya tai shiru Jibrin yace ke wai lafiya kika kirani da wanan ranan haka, Hmmm ai kaima kasani don Alkah dai mubar wasa muyi maganar gaskiya yau, Jibrin ina mutumin ka ne wai tafada tana yar dariya kasa,kasa, Duk da ya gane watake nufi amma sai ya dake yana ce mata, Wai wa kije nufi ne sadiya, haba Jibrin don kaga ina mutuwar son abokin ka shine kake min haka, Wai har yanzu ki na ga son shi ne,, Sadiya ? Murmushi tayi, tace ai kaima ka sani Jibri, ka dai ki hada mu da shine kawai, Tausada taba jibrin don ya dade da,sanin cewa sadiya tana son Yusuf da da dewa, Amma yau sai ta ba shi tausayi saboda irin yadda yaga,tana mutuwar son Yusuf, arayuwar ta, Kin gane ne sadiya ki bari zan mashi magana insha Allah zaki kiji ko mai, a guri na, Sadiya ba tasan lokacin da ta fara zabgawa Jibrin godiya ba, Murmushi yai mata kawai, yana mai jin tausayin ta, Don da da farko haushi take ba shi akan zancen amma yanzu yaga da gaske takeyi son Yusuf takeyi, Jibrin bai ja wani dogon lokaci ba gurin tuntubar Yusuf da zance inda yakara mai bayani akan Sadiya, din, Yusuf bai wani bashi amsa ba cikakke sai dai yar murmushin dayayi wanda murmushhi wani part ne na rayuwar shi Don haka sai Jibrin yafara tuntubar Ànty Dije don yasan cewa ita abokiyar shawar Yusuf ne kuma, Kwarai Anty tai murna da wanan labarin don har ta kasa boye farin cikin ta, Rana ake kodawa saboda giragizai da suke yawo a sararin samaniya, Garin sai yadauki zafi gashi NEPA sun dauke wuta, A gajiye maryam ta dawo, saboda zafin ranan da akeyi duk ya kode ta, Ànty Dije wace ke ta farin ciki da labarin da Jibrin yaba ta tana zaune da Abubakar sai waka take mai, Hakan yasa maryam gane cewa, Anty ta cikin farin ciki yau, Takalmin da tasa na Tommy, shi take ko,karin cirewa, Ta wallwale daurin dake a kan ta da tayi na rolling, ta wurga a saman kushin, Fridge ta nufa ta dauko, ruwa a cikin leda sanan tadawo inda anty take zaune ta zauna tana zukan ruwan a hankali, Sannan tai yar ajiyar zuciya saboda sanyi da taji yadan ratsa ta alikacin, Anty naga kina wani farin ciki ne yau tunda na shigo, ? Marya na kokarin, mikewa tsaye, take tambayar yar nata, . Kedai maryam kani na ya kusa zama ango shima, Wake nan Anty ? Maryam ta tanbaya a lokacin kai tsaye, Yusuf mana, Taba ansa a takaice, Maryam wace a lokacin ta kusa kai wa tsakiyan falon sai ta juyo tana yiwa Anty nata kallon mamaki kawai, Yusuf fa Anty ? Shifa inji anty sai kokarin yiwa Abubakar wasa takeyi, Cak Maryam ta tsaya don karasa sauraron zancen da anty ke fada mata, Wallahi ke dai maryam ina wanan cousin sister din ta Jibrin da muka gani a gidan atika, Dammm Maryam taji gabanta ya bada sai dai bata san ko na maye ba dai, Sai kuma ta yake baki tana cewa Allah yasa dauka,sirious, dai, Daga haka tasa kai ta wuce zuwa cikin dakin ta kawai, Tana shiga daki ta fada saman gado ta rub da ciki , A,cikin kasala ta dan jawo filo zuwa kan ta, sai da ta kwanta da kyau kanta na sama yana kallon silin sanan . Maganar Anty yafado mata arai, Azuciyar ta tace kai badon aure hafin Allah bane da sai tace, gaskiya basu dace ba sam, Ita wanan Sadiyar da bata da marmari sam duk yadda kake bata iya gaishe ka ko kuma ta nuna ma sakin fuska, Ire iren tunanen da taitayi ke nan har zuwa wani lokaci, Don kan ta tamike zuwa watsa ma jikin ta ruwa don ta dan ji sanyi, Abinci da take dauki ta dawo ta ci sai gashi har da tuni anty tai mata , Duk yinin yau a kasalance maryam ta , wuni Amma bata san ko may ke damun ta ba, kawai dai sai taji batajin wani kuzari, Don haka, tun shiganta daki, bata kara fitowa ba har dare., Anty Dije ce taga cewa maryam bata fito ba don haka ta, tashi ta aza masu girkin, dare,. Anty Dije ce,ta matsawa maryam ,da cewa tafito su ci abinci, Dole badon taso ba tafito , Abinci kadan tazuba a plate, amma duk da zaman shi kadan ta kasa cin shi, sai tsakura takeyi tana cusawa,, Ido Anty ta zuba mata har na wani dan lokaci ,can ta nisa tace, maryam may ke damun ki, ne wai, Cikin jin wani irin nauyi maryam tace, ranan da na kwaso ne, yasakar min ciwon kai, Wayar Anty ce tai kara alamar kira , Maryam wace, ke kusa da,waya itace ta mikawa Anty wayar, Da dariya Anty ta karba sallama tana cewa mun kusa shan buki ashe Yusuf,? Magana sosai sukeyi da Anty ida maryam ke jin yadda Anty Dije take lalashin shi, akan ya daure ya yi wanan abin da jibrin ke kokari ganin ya hada, Maryam dake zaune a kasa, saman ties, sai ta dan kai kwance, a bayan kushin, Ta sa kan ta, saman kujerar da take zaune a kusa da shi , Murmushi, tayi tana wasa da Abubakar wanda ke ta washe baki, a gaban ta, So,sai suka dauki lokaci tana kwantar wa Yusuf da hankali akan kudirin su, Acewar Antyn wai yin auren zai rage mai damuwar shi sosai, Su,kayi sallama Anty Dije ta dan kalli inda maryam take tana wasa da dan yaron, Tajima kafin tayi barci a ranan, bayan tabar falon tayiwa, anty ban kwana, Alwala ta daro ta dinga jero nafilfilu masu ma,ana, Sai ji tayi zuciyae ta yai wasai, kamar ba ita bace ranta yake a jagule, Sai a lokacin ta, maryam ke ji a ranta bata jin komai gamay da zancen da akafada mata, , Yusuf ya iso kofar gidan Anty Dije, bayan sati biyu, da misalin karfe biyar na yamma, Da sallama ya shigo cikin gidan alokacin maryam tana zaune cikin shigar shadda kamfala, Shiri takeyi zata gurin bukin wata abokiyar ta na tun secondary school, Zaune ta a saman kujera yar tsuguno tana ta faman gyaran fuska, Dawani guntun broking mirrow, sallamar shi ce tasa ta tsaya wa daga fente fenten fuskan da takeyi, Da yar fara,ar ta, a fuskan ta ,tare shi Sannu da zuwa ta iya furtawa a hankali amma tana mai dukar da kai,, Kallo guda yai mata yaga yadda ta koma kamar wata, classic baby, Yaji wani yarrr amma sai bai ba da wanan abin yaji wani ma,ana ba, Kafin ya karba mata anty dije ce tafito, a lokacin, Ànty Dije ce ta fito daga ciki tana dariya da murnan ganin Yusuf a wanan lokacin, Oyo, yo da mutane Lagos ne ko Abuja, sai da yai yar dariya na nuna farin ciki, yace ai nafi zama a Abuja yanzu, Maryam ce ta tashi daga inda take ta dauko yar jakar kayan make,up din ta, Tagaban Yusuf tayi bi inda kamshin nan nata kamar kulun yadaki hancin shi, Ga dikin purple shadda kamfalan da tasa ya karbi jikin ta, tsab, Daidai da zaman shi a lokacin ta dauko mai ruwa a cikin gora, hade da cup A gaban shi ta dire kayan karo nabiyu kenan da wanan kamshin da ta budawa jikin ta yasa shi lunshe idon shi, Thanks ya,furta a hakali kamar yadda ako yaushe maganar shi mai rowa ce, Idon shi a lumshe kamar mai barci taji muryan shi yana cewa, maryam ga key a,dauko wa an nan kayan dake cikin motar, Wani irin haushin taji don tasan zai bata mata lokaci ke nan, Da sauri ta kalle shi tace saidai kila ba yara a wajen ko, ? Daga shi har anty ido suka zuba mata dn jin maganar ta , Wanda ya nuna tana uzuri ne hakan yasa tace masu ba yara, Anty Dije tace maryam sai kace ba wace iyakarta cikin kwantagora ba, Wallahi Anty bana son in makara ne saboda sun riga sun sa cewa bazan zo ba ma sam, Nikuma ina son basu mamakine su ga na riga kowa isa gurin, Takara sa fada cikin shagwaba kamar yar karmar yariya mai shirin yin kuka, Da ga ida yaje zaune ido kawai ya zuba mata alokacin , Don yadda take maganar kamar wata yar goye, Anty ce tace inbanda abinki maryam tun da ga sauki Allah yakawo maki kawai da kin kwaso sai kibi Yusuf ya sauke ki tun da hanyar su zaki bi, Kai kasa cike da jin nauyi likamata bin shi da antu tayi tace, Ai basai na bishi tun da bai tashi ba kawai zanbi motar kasuwa, Muje in sauke ki idan nadawo zan samu yara su sauke kayan, Wani irin nauyi maryam taji a lokacin sosai, don jin ansar shi, Ba musu dole ta jawo gyalen ta ta yafa tare da murza mai turare tako ina Tsaye yake a bakin motar shi yana waya fuskan shi na kallon ta cikin gidan nasu, A nutse ta ke takowa zuwa ida motar shi take, waya yaje yi amma kallon tsab yake kara mata , Tsayawa tayi daga dan nesa dashi kadan ta yadda bazata ji may yaje cewa ba, Yagane nufinta don haka ya tsaida wayar yana ce mata bissimillah mana mutafi ko, Mamakin irin saurin kwashe dabi,un shi na hausawa,musulumai da yayi da sauri takeyi, Bayan motar ta tukara inda yace mata haba dai ai bayan ba guri duk kayane a ciki, Dawo gaba kawai ki shiga ina ga zai fi, A hankali ta saje hannun ta nufi dayan bangaren ta bude, Kamar kullun sanyi da kamshi dai yana nan a motar nashi, Ya na kokarin tada motar ne yake ce mata ina,ne gurin da zaki din,? Tace mai MARAFA parks, A takai ce tai maganar don haka bai kara tambayar ta ba, A marairaice kamar mai shirin kuka tace, don Allah ina son zan dan tsaya Blue, sea, super market, Batare da ya kalli inda take ba yace mata ok kawai, .,,,,,,,,,, , ZEEE MAKAWA,,,,,, [3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: .🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, UBANGIJI ALLAH YASA MUGAMA DA DUNIYA LAFIYA BAKI DAYAN MU YAN UWA MUSULMAI,,,, 👏👏👏👏👏👏👏 Dan zagayawa take yi, cikin super market din, tana dan dibawa ko zata samu, abinda zata saye a matsayin gift , duk da bawai wasu kudine masu yawa acikin jakar na taba, Layin sai,da kayan kamshi take dan zagayawa don dibawa, Duke take tana kokarin ciro wasu set na shafa, irin ta mata, acikin wata, yar kit, "Yan mata ya kike kwana biyu, ? Muryan take tunane a ina tasan shi ne wai, don ko bata waiga ba tabbas tasan wanan muryan, Bashir Alhasan ne tsaye da wasu kayan da mafi yawan matasan maza hausawa ke sawa a yanzu, Tunane takeyi a ina tasan wanan fuskan ne wai, kafin second ta tuno, dashi. Bata san lokacin da ta sake wani dan munrmushin da iyakar shi fuska, Ina yuni tace cikin yanayin muryan nan nata,, Yar kwaikwayon ta yayi hakan yakara sata sake wani lalausar murmushi again, Tsayuwar shi yagyara yace ai nasan dama kida baki fada min inda kike ba wata rana zamu kara haduwa ne, Yakara zancen, yana mai dan rausayar da kai, kamar wani kara min yaro, So ya kwana biyu ya karatu Maryam Abdullahi ko, Yana mai mata wani kallo irin na wayyaun maza, Kafin ta bashi amsa yakara jefo mata wani tambaya, May a kazo saye ne haka, ? Bata bashi ansar ko guda ba sai dai yar murmushin da takeyi a kasa kasa, Set din kayan, da ta dauka ya mika hannu ya karba yana dan karanta sunan shi, Yace da alama dai gimbiyar gift take dibawa ko, Hannu taga ya mika can ciki ya dauko wani babban set mai kaya kala kala cikin kit din, Yace ina ganin ai wanan zai yi ko, Maryam wace sai binshi da ido take don kara tan,tance halin shi, Sai ya dan daga kai saman yana karanta wasu set haka, dake gurin, Yadawo da kanshi yana mai kallon ta fuska a sake yace bazamu layin Sweet bane ko? Kai ta girgiza mai alamar a ,a bazata ba, don haka yadan daga kafadar shi alamar ba ruwan shi, Zan wuce ta furta, a hankali, kamar mai maganar rada, Ok muje ko yace mata tana kokarin ce mashi ai ya barshi, Sai ganin Yusuf tayi tsaye da alamar tun tsayin su gurin yake kallon su, Tsaye yake a bakin wani da kantar kaya yajin gina da wani bango dake gurin kafar shi a harde, acikin wani, Biye Bashir yake da ita, duk tawani kunya da ganin su da yayi, atare, Suna tafe sai yaba kyawon kwaliyar ta yake yi yana kokarin cusa ta gwaunatin gare ta, Sun kusa kaiwa inda Yusuf yake tsaye cikin dakewa sai wayar shi yaje latsa, Maryam ta dan kalli Bashir,ta juya inda Yusuf yake tsaye tace, Ga yayana ku gaisa dashi, Wani kallo yai wa Yusuf na second, inda yagane cewa ba karamin mutun bane, don komai na jikin Yusuf zaikai kusan million, guda, Yana yar dariya yace au kice min bake kadai bace dama, Hannu ya mikawa Yusuf suka gaisa, sai dai Yusuf din,ya, na yin hausa sai Bashir din ya dan waigo maryam, Tagane may yake nufi a cikin style ta kada mai kai alamar eh, Amma tunda nayi ni,yar biyan kudin, wa yan nan kayan ina fatan cewa yayan mu zai bari in biya ? Fuska aba walwala, Yusuf yace wa maryam indan kun gama sai ki samay ni a mota, ina jiran ki, Daga haka ya juya zuwa waje inda suka aje motar su, A tare suka fito dafa cikin plaza din da bashir wanda motar shi take aje a gefe guda, Gurin motar Yusuf Maryam ta nufa ganin haka Bashir yadan fidda idon shi yana mamaki hafin maryam da wanan guy din, Yusuf na kallon su daga cikin motar shi dake makale da tin tak glass, Sun kysa kaiwa gurin motar maryam taja tai tsaye tace mashi, to na gode kwarai Allah saka da alheri, Yadan sa key holder din shi ya sosa kan shi, Sai kuma mukara haduwa ko maryam makarasa zancen mu ko ? Da,sauri maryam ta dan kaleshi, tace yaushe kuma zamu kara haduwa ai ko yau sa,a ce, Sai,da yai yar dariyar maganar ta, san,nan yace, aini dama ko yaushe a cikin sa,a nake, Kai kasa cike da jin nauyi maryam tace to shi ke nan nagode badamuwa ki, sallamar min da yayan mu, A nutse kamar kulun ta isa gurin motar inda tadan kwan kwasa mai glass, , Tana shiga motar yataya suka harba saman titin, sai dai a hankali yake tukin shi Duk da kasan cewar motar babbace amma hakan bai,sa,shi yin gudu ba, Sun dayi tafiya kadan, batare da, yawaigo inda take ba yace, Wani, kuma sabon mayaudarine kika,samu, haka ? A cikin mamaki take kallon shi ido a zazzare Kallo, mai kama da harara ta yayi yace, gaskiya maryam ko wanan bai dace da ke ba, sam wallahi, Kanta aduke tai shiru saboda wani irin bakin ciki da ya tokare mata mokoshi, Ya dago ya kalle ta idon shi ya canza zuwa bacin rai, Haka itama maryam domin maganganun sun daga mata hankali, Idanu a runtse tana jin wani irin bacin rai, da kunar zuciya, Haba ya Yusuf, ai wanan maganar bai,dace ka fada min ba, Cike da mamaki, ya ware ido yana kallin ta don sam bai dauka maganar zai sa bacin rai haka ba, What maryam bakya son a fada maki gaskiya ne, ? , a,fusace kamar wace zatai shirin kuka, tace mai, haba dai daga ganin mutum kawai zaka yanke man hukunci akan shi, Yakamata ace katambayeni bayani akan shi bawai kawai a yanke mun hukunci ba Ya Yusuf ya,kamata ace kana cikin wa yan da zasu shedeni, Kamar yadda kake tuhumar ina hurda da yan duniyar samari, Ma,ana nima din yar duniyar ce ke nan ko,? Murmushi ya yi kawai har zuwa lokacin da ta kare fadar maganar ta,, Hakalin shi ya mayar a,titi, sanan yace, Don nasan cewa,ke yarinyace karama , duk sun fiki wayo da sanin duniya, Sam baki dace dasu ba gaba dayan su ,bai,kamata ace kina tsayawa dairin su ba,, Daga haka ya mai da kan shi a kan titi sosai, bai kara,bita kanta ba,. Saida suka kawo unguwar ya tambayi maryam tai mai kwatance a takaice , Kofa ta bude tana kun,ku ni, tana cewa wanda ke tare da irin su Aisha da sadiya ba ace mai ya bari ba sai wace ba ruwan ta za,a sawa ido, Lock din motar ya dan na tayi tayi ta bude ta kasa sai a lokacin ta waigo in,da shi,ke zaune, Kamar ba shi take jira ya bude mata kofa ba, sai kawai,ya kama lalabar wayar shi, Cikin murya mai nuna karaya zuciya da kuma kuka, tace mai, Ina son zan fita ne Bai juyo ya kalle ta ba, tankar da dutse take, Sai da yagama taba wayar shi san nan ya dan,na unlock, motar ta bude, Ran ta a bace ta sa kai kawai tafita batare da ce mai komai baya, Bayan ta ya bida kallo a hankali, sai kuma yai saurin kau da kan shi yana mai cewa Astangafurllah, Ganin irin tai makon da yai mata bai kamata don ya fada mata gaskiya ba haka tai fushi tafita ko godiya babu, Ta dan waigo kamar mai rada tace mai nagode Kai kawai ya kada mata batare da cewa komai ba ya ja motar shi yabar gurin, Duk da taron bukin yai kyau ya kawatar, ga kuma abokan su na tun makarantar secondary sun hadu, Rayuwar maryam a bace yake saboda duk kusan ba yan yan mintina sai ta tuna da zancen Yusuf, Har yanzu kanta ya daure ta rasa gane may maganar shi take nufi ne haka, Da zaice mata wai ta kara samun wani mayaudari, Yana nufin cewa A,A din ta mayaudari ne ko may ya ke nufi da hakan, A haka tai tawa yan uwa yake don kada su gane halin da take ciki, Zaune su ke su uku afolon gidan Yusuf din suna shawaran abin yi, Su ke ta shawaran su shi iyakar shi sauraran su yake yi, Shi iyakar shi, yace masu ummh ko eh ok haka yayi, Saida,duk suka gama tsarawa san Jibrin ya dauki wayar shi ya kira Sadiya yana sheda mata zancen zuwan su gidan su yau, Yusuf wanda ke duke Sai a lokaci yai magana ya ce, Jibrin baka ganin cewa ya dace mu tun tubi iyayen ta tukun muji ra,ayin su kamar yadda shari,a ta tanadar Amma sai Jibrin yace mai wanan ba matsala bace don yasan cewa za, yarda in da ta fanin shi ne, Yau itace ranan farko da Yusuf fara,zuwa gurin sa,adiya hira, A hankali yake nazarin yarinyar sai,dai gaskiya ya du, ba ba wani makusa ga yarinyar, Kamar yadda ya za ta zai samu matsaloli a gurin ta, gaskiya a yadda yake gani ta, Da safe yazo gidan Anty don ya karya duk yai rana yau da zuwa, Anty Dije tafito cikin shirin ta kasancewar wanan karon ya Illiya yana gari, shima Nan suke hira da Anty Dije zancen yana bata labarin zuwan shi a daren jiya, Dariya sosai anty dije ke kwasa don yadda irin yadda ya yai ta mausu sheri ma, Wayar anty ce yai kara a lokacin shine ya katse masu hiran da suke yi, Hiran da maryam ke sauraro da ga in,da take kwance saman salaya ta, Innalillah taji anty na na tawa a lokaci guda, da sauri maryam tafito waje da sauri, Tana jin anty tana cewa injin baiji ciwo ba, dai ko, dausauki sosai, ?? Maryam wace tafito sanye da wani dogon rigaba English , taitsaye tqna mai son jin ko may yafaru Sai alokacin Yusuf ya,ganta don lokacin da sukayi wanan maganar bai kara sata a ido ba, Shima Yusuf ido yakurawa Anty don jin ko may ye matsalar, Inda yake anty ta kalla tare da kara kallon Maryam, Sanan tace wai baba ne sukayi accident da mashin a hanyar shi tazuwa kasuwa, Maryam tace subbahanallah injin da sauki dai Anty? Tace wai suna asibiti za,a diba su, kusan tare suke tambayar ko wani asibiti ne, Bai kara wani lokaci ba sai mikewar da yayi yana cewa bari je in gani zai fi. Yasamu jikin da sauki ssai da gurjewa yayi a hannuwa da kafa, , aka dan mai treatment aka sallamo shi, A, gidan baba duk hakalin su yadaga sosai sabo suna gudun kariya, Da taimakon su Yusuf ya shigo cikin gida ya na dan dan gyasawa, a hankali, Anan suka samu su Anty da maryam gidan sai faman sannu akewa dan tsohon, A hankali yake zayyana masu irin yadda al,amarin yafaru Kowa na ta mai fatan alheri da Allah ya tsare gaba, Daya daga cikin yaran nashi wata maison kama da Anty Dije tace Baba nidai daka hakkura da zancen zuwa kasuwan nan wallahi, Ba yadago kai a hasale yace idan nabar zuwa uwar wa zamu ci agidan, Sim sim ta noke don gudun kar baba ya aza mata fada Rana har bayan azahar suna gidan mahaifin su basu dawo ba, Kasuwa ya shiga inda yasiyo wa baba kayan kara jini, Alaiho, da Anta mai yawa sai kwai, tare da fruit da madara, Zaune baba yake ya na sallamay sallah da yasamu yayi, Idon shi yakai ga kayan da yara ke shigowa dashi a cikin leda, Idon shi kem a,kai don ganin irin kudin da aka narkar Mai sakon ne ke fadawa baba cewa daga gurin Yusuf ne sakon yafito, Duk wanda ke gurin sai da yai dariyar wanan dan tsohon, da abinda yace, Wanan duk wa zaici sune shin waya yar shi Da bata karkare kai su maryam shekaru ba tace baba ai muda kaine, Da,kuwa yai mata yace mata karbi naki yar nema kawai Inda anty take zaune tana bawa danta nono baba ya waiga yace wanan barnan dukiyace duk azube alokaci guda acin ye, ? Dariya duk wanda ke cikin gidan yasa don jin magannar da yayi, Tunda safe sai yan zu ya shigo gidan inda ya samu maryam tana girki a hakali Yai mamaki kwarai da yadda ta gaishe shi, saboda tun, wanan lokacin da yai warning dinta, akan samarinta, Maryam tace ma Yusuf sannu da kokarin Allah saka da alheri, Albarkan iyaye nake nema don yafi min amfani, Don haka sai ki daina min godiya addu,a kawai zaki min nima mahaifina yazama tankar na kowa, anan gaba, Wani irn mugun tausayin shi maryam taji alokacin, kamar tayi kwalla, ZEEE MAKAWA [3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: .🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Ubangiji Allah ya taimaki musulmi duk inda yake, Allah ya karawa Annabi daraja,👏👏👏👏👏 Zaune yake a falon gidan shi yana kokarin balle bottom din rigar ta wuya, A hankali yadauki kafar shi guda zuwa sama wani dan stol, din katako dake falon, Bayan shi yamar a makatin kujerar a hankali yana mai sauke numfashi kamar wanda yagaji Idon shi yadan lumshe a hankali, yana mai tunanen inda yafito, Shidai yasan cewa yanzu musulmi yake mai sallah farilla biyar a kowace rana Amma kuma ga yadda yaga al,adar bahaushe ko musulmi zai ce bai mai ba, Saboda wanda bai tuba ba kafiri arne zasu ce mai suna mai nuna kyamar shi Sai kuma gashi wani bakon al,amari da yake fuskan ta yanzu nuni da cewa, da ake mai wai tubabbe, Murmushin bakin ciki yayi ido arufe wani irin mugun bacin rai yaji, May ya rasa ? may ye bai yi daga fannin addini ? May za,a iya gwada mashi a yanzu ? Amma sai ga shi a cikn taro ba ko boyo ko kawaici, ake cewa ashe shine tubabben nan, May kuma illar wanda ya tuba kawai, ya shiga cikin ku, Shin may amfanin nunawa mutane hanyar tuba, da ake yi, Sai kayi kuma adinga kyamar ka kamar wani mugun abu, Karar wayar shi ce ta katse mai tunane Grandma ce ke magana dashi, Bayan sun gai sun danyi hira kadan take tambayar shi ko yaushe zai dawo saboda wai, tana son suje gida gurin festival, A fili ce mata yayi zai dawo zuwa weekend insha Allah sai su fara plan din tafiya, Amna suna gama waya sai yai yar tsuki don in akwai abin da yai hating tun farko shine irin wanan bukin festival din, Inda mata da maza zasu hadu adinga yin abubuwa tankar tsafi, a gaban wani halitta, A gurin ake hada wasu aurataiyan inda nan samari da dama suke ganin yan matan da suke so, sai a kulla alakar aure, Nocking din kofar shigowa yaji ana yi a lokacin abinda ya sa,shi mantawa da komai ke nan Ya mike don yadiba yaga ko waye, ? Aisha ce tare da Amina ,ko,wacen su tasha kwalliya cikin material dinkin buje da riga sun dane masu jiki, Ga gashin kari sun kara sai kace, wasu diyan kafiran da suke cewa, Hannun su duk an painte shi da ja kumba, ga wani eyelashes sun zuba, Haka kawai sai yaji wani haushin ganin su a hakan, Bakaramin godewa Allah yake yi duk ya tuna cewa wani abu bai taba shiga tsakanin shi da Aishan ba, Kirjin su duk yawani bultso tagaban rigar su kusan duk rabin nonon su a fili yake Sai dan gyalen da suka yarfa a wuyar su kamar sarka, Takalmin su ba,a maganar tsinin shi saboda tsawon shi, Kokarin shigowa da takalma suke yi amma sai ya dakatar da su da cewa, Haba sai kace wa yanda basu san darajan gidan musulmi ba cewa sallah zata iya riskan ka,ako ina acikin gidan ka, Ya cew Amina ki daina biyewa wanan pls yana mai nuna Aisha da hannu Yace ita ta riga ta kuna bata gudun yin kauri sam, Darita tai mashi a lokacin da take kokarin cire takalman ta, daga kofar, Kokarin rungumashi takeyi Amma sai yadan ture ta baya kadan yana mai ce mata baki da kunya fa ke, Yanzu fa nagane cewa baka son inadan taba ka inji dumin jikin ka Tafadi tana kokarin zama saman kujera dake fuskantar inda taga yana son zama, Yaushe rabon da indan yi hugging din ka sai kawai jayewa,? Cikin mamakin irin bushe fitilar ta yake kallon ta, Sai dai bai iya ce mata komai ba yadan yi murmushi kawai, kamar yadda ya saba yi, Mun,zo jiya baka nan na san cewa kana can gidan wanan munafukar sister karyan ka, Ciki dakewar murya ce mata look bana son wanan halin sam wallahi may tai maki, Ita warinki ce da zaki dinga yi mata haka, Jifa maganar ta kawai nayi yanzu amma kana kokarin cimin mutunci akan ta, Ai nasan duk plan din ta akan ka wallahi so take ta mallake ka ta aura maka wanan kaunar nata mai kama da bafullatanar Niger, Kai, inji Amina wace maganar kawar nata yasa ta jin kunya a takaice, Duk kallon inda Aminan take sukayi cikin wani irin magana take cewa aiko yarinyar nan kaunar Dijen Illita costume tana da kyau, Ba ita bace, A,A ke nema saidai uwar shi ta hana shi, tace zata hada shi da yar uwar shi, Yusuf wanda ya nuna bai wani damu da hiran da sukeyi ba don wayar shi ya hau latsa Amma sai maganar cewa ba za,a bar A,A ya auri Maryam ya tsaya mai a rai, Ba zai aure ta ba to may yake zuwa yi gurin ta ko yaushe Gaskiya wanan maganar abin bincike ne sosai, Kwance Aisha take sama kujerar tawani yi dai,daya da kafar ta, Aisha ya ce cikin murya da tankar a tashi ba yau don yadda ya furta ta, Look bana son irin wanan dabi,u sam wallahi hakan baida wani amfani a gare ki a matsayin ki na diya mace, Bana son kina zuwa wanan gidan idan nazo kina min irn wanan rashin kamun kai, pls ? Da yar mamaki ta mike zaune da niyar yi mai magana amma sai yadakatar da ita da hannu Alamar bai son jin komai daga gareta again don tun da tazo batwi wani abin alheti ba, Ganin yadda fuskan shi ta nuna ne yasa Amina cewa Aisha, Ke ko gaskiya Aisha haka fa baida kyau wallahi, Ita sister tawa da kike cewa ta karya tafi min ke sau dubu wallahi Domin zama da ita alheri ne a gare ni sosai ba kadan ba Ki fada min zama dake abin amfanin da na samu akai, Tamike zaune da kyau dan yau jin maganar shi takwyi ba taushi, Tai wani far da ido tace mai laifin waye idan baka samu karuwa daga gare ni ba, Yawani kada kai ya ce, Allah yai min tsari da irin taimakon ki, Zance wai za,a hafani fa kaunar anty kuma ki sani cewa zancen aure na ya kawoni wanan garin ganzu haka, Daga haka bai kara magana ba yasa kai ya bar falon cike da kunar rai, Kallon mamaki suke mashi don basu taba tunanen cewa zai iya rufe ido haka ba, Maigadin shi tare da body guard din shi suka shi go falon suna ce masu zamu kulle gida kufita pls, Ikon Allah inji Amina tace yanzu dan Allah har ma korar mu akeyi haka, ? Yau kimanin wata biyu ke nan inda zancen Yusuf da Sadiya sai kara girma yakeyi, Bayan har Aisha ta sa an binciko mata ko wace yarinya ce Yusuf ke shirin aure, Tayi mamaki kwarai don jin abinda ta tuhuma gurin anty ba gaskiya bace, Wanan shigowar don shirin azumi dake tafe yayi wa garin , Amma sai kuma ya samu cewa mahaifin shi baida lafiya A gurin makwacin su yake ji wanda kusan ko yaushe yana fada mai abinda gidan suke aciki, Gidan nasu ya tafi kai tsaye bayan ya iso inda ya samu duk mahaifin nashi ya,ramay tankar wanda ya Duk yadda yaso yaiwa dan nashi cin fuska sai ya kasa saboda kwar jin da yai mai a idon shi so,sai, Yusuf din ya murje ya zama wani matashi hamshaki, dagani basai an fada ma ba, Da kanshi ya kai shi gurin likita don yadiba shi aga ko may ke damun shi, Tsumu, tsumu ya na rike da hannun Yusuf din har gurin likita Inda a karshe aka tabbatar masu cewa yana dauke hawan ji, ne,, Sosai Yusuf yai ta mai magana cewa,ya daina wanan yawan tunanen, da yake yi kada yai mai illa, Sai da ya tabbatar da cewa yasha duk wani da likita ya bashi kuma yai ma wa yan da ke a tare dashi magana akan su kula dashi, so,sai Sai bayan tafiyar shi ne yan church din sukazo cikin fada,suna cewa wai may ya kawo shi, gurin mahaifin shi, A gaskiya su sam ba, su yarda da wanan ba, tunda yace ba ya tare da su, Don haka wai sai ya daina zuwa gidan nasu, Maryam wace ke zaune tana, gyaran kumbar kafar ta, Wayar ta na gefe guda ta sa Kira,a tana dan bi a hankali, Yusuf din ne yashigo da sallamar shi inda duk ita da yarta suka ansa mai sallamr shi, a lokaci guda, Wani yaro yana biye da shi a bayan shi dauke da wani leda da ke dauke da ga hannun yaron, Maryam wace tunda ta daga kan,ta da ta gaishe shi bata kara kallon inda yake ba , Muryan Anty da take daga wasu shaddadoji masu tsada da yakawo wa anty, Don ta tayashi dibawa saboda ya kai a dinkawa Sadiyar shi, A yadda suke zance da anty sai yana bawa maryam mamaki saboda irin yadda take gani daya fita waje yadda mutane ke wani girmama shi, Anty Dije ta shiga wani wasa sadiyar tana wani yaba ta ga Yusuf Tana kokarin kafa gwaunatin ta gare shi shiko sai wani lumshe idon shi yakeyi, Don dai a gaskiya da farko ba,wai wani son ta yakeyi ba, Don dai kawai tana yar uwar Jibrin ce yasa ya yardda da zance, Sai gashi yanzu sannu a hankali yafara jinta ajikin shi, Daga inda maryam take zaune tai wani dan guntun tsoki, Yusuf tunda Allah yasa yanzu kun yi nisa ya,kamata ace yanzu zancen ya fi ni girma, saboda iyayye su shiga har kan duk da dai sun san da zancen, Yusuf dan rau saya kai yana maijin dadin irin kulawar da Anty Dije ke yawan bashi, Anty Dije tace hankalin ita Sadiyar ma zaifi kwanciya nake gani, da hakan, Yusuf zai yi magana ke nan sai jin muryan maryam sukayi gabadayan su tana cewa, Wai Anty ita wanan Sadiyar daki ta zancen ta ako yaushe, May kika gani a gare tane wai, mace wace ta zubar wa kanta da aji, tace wai tana son namiji, Har a dinga wani zuzuta zancenta sai kace wata can , Gata wata garmakyakiya da ita fuska ba fara,a , takare zancen dayin yar tsuki a karo na biyu, Daga haka ta duka taci gaba da yankar farcen da takeyi, Kamar ba ita bace tai wanan maganar da ta barsu suna mata kallin mamaki, Murmushi Yusuf ya wanda har ya ba da yar sauti, Hakan yasa maryam dago kai takalle shi don jin irin abinda yayi, Anty Dije tace wanan kuma wani zance ne kawai na daban maryam a mma ai ko ba tada makusa sadiyar, Kallo mai kamar harara tawatso gefen da suke kamar za tai magana sai kuma ta dukar da kanta taci gaba da abinda takeyi, Saida ya gyara zaman shi da kyau yadan kada kafar shi sanan ya kalli inda take yace ma, Anty ramawa Maryam tayi don na fada mata gaskiya akan samarin ta ranan, Batai magana ba sai shiru da tai masu sai kace bada ita suke ba, Anty dije ce tace hummmm maryam halinki sai ke wallahi, Ba,a sukar aure fa inda ba zaka gyara ba to kayi shiru akai Sai a,lokacin tai magana tana mai mikewa tana kakabar zanin ta da wani kyale, Tace ai ni gaskiya na fada anty don sam ba suyi matching ba da ita, Anty Dije wace taji haushin zancen kaunar nata tace, Aisai ki samo mashi wace sukai machin dashi ina ga zaifi wanan jayayar taki, Daki tashige abinta tana turo baki gaba don dai ita tafadi ba kuma yadda za,aiyi da ita, Duk da dare ne ya,kamata a ce yai barci by now Amma sam barci yaki zuwa mai sai ma maganar maryam dake kokarin yi mai yawo a kwakwalwan shi, Maganar maryam din gaskiya ne duk da ya fahinci acikin gatse tai mashi su, Amma shi kanshi yasan cewa sam basu dace ba tun farko , Saboda Jibrin kawai yadaure har haka tafaru a tsakanin su, Tunda Jibrin din ya nuna yana son wanan abin shikuma bai iya,watsa mai kasa a ido,, Juyawa yayi dayan ban garen yana mai kara rintse idanun shi stil maganar ce ke mai yawo akai,har yanzu,,,,,,,,, 👏👏👏👏👏👏👏👏 Dan Allah kuyi hakkuri masu cewa wai basu gane abinda nake rubutawa, wai bani rubutu da kyau ku yi min afuwan pls banda enough time ne da zantayin editing ZEEE. MAKAWA [3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Assalamu A,laikum yan uwa musulmai, fatan alheri agare ku ko dayau she, Wanan daren Alhamis din son in amfani dashi gurin mika gaisuwata tare da fatan alheri, ga duk masoya wanan novel na furen juji da,nakeyi, Kaunar novel din ku na nuna kaunar ku zuwa ga addinin mu ta musulunci maidaraja, Ubangiji Allah ya kara haskaka maku rayuwan ku, Allah yakara rufa asiri nagade,,,,,, Zaune yake saman table din dake cikin office din shi yana duban wasu takardu, Sai laptop din shi dake a saman table din gefe guda ajiye, Yana rike da biru sai ticking din wasu daga cikin abinda yake diba a cikin takardun yake yi, Kada kanshi cikin mamaki yakeyi don sam bai taba tsamanin cewa abin ya kai haka ba, Biron dake hannun shi da pepper ya aje saman table din, Komawa yayi da sauri saman kujerar da yake zaune da farko,cikin sauri ya fara dan,na computer, Hannun shi guda da sauri yake sarrafa computer din shi don son ya tabbatar da abin da ya ke gani, a rubuce, Bakomai bane face zunturu tun ribar kudi da company shi ta samu, Sau uku yana furta Subbahanallah Wallahamdullah Wa,lah,illaha,illah, Allahu Akbar, Sai kuma yadora da fadar Hamdallah, Komawa yayi ya dafe kanshi da hannun shi duk biyu kamar mai jin wani ciwo ko tunane, Zubur ya mike yana mai daukar makulin motar shi, Yanufi hanyar da zai sada shi elevator, don ya yi saurin sauka, Tuki yakeyi a hankali sai tune yakeyi yanayi yana kallon gaban sa, Gidan wani limamin massalacin da yake yawan bi sallah ya tsaya, Zaune yake gaban malam cikin ladabi yakewa malam bayanin irin riban da ya samu a cikin wanan lokacin, Saida malam yai gyaran murya sannan ya fara magana acikin kwanciyar hankali yadda Yusuf din zai fahince shi, Komai na gamay da zakka da kuma sadaka fissabilliha malam yai mai karin haske akai,, Godiya yaiwa malam yakawo alheri mai yawa yabawa malam din, Bai koma office ba saboda yana da abubuwan da yake da bukatar yi kafin dare, Ga fahintar shi ga bayanin da malam yai mai, shine, cewa zaka bayar da ita ga wanda ke a cikin bukata yafi, Ko kuma ka taimaki wani ta yadda mai,shi zai iya mikewa, Ba kamar yadda yaga cewa akasarin madu kudi suna rabon zakkah a yanzu ba, Da za ace sai tallaka yabi layi adinga bawa kowa dari biyar biyar ko yan dubu guda guda, Inda zaka ga mutane suna ta tururuwa zuwa karban zakkah gidan masu kudi, Inda har ko kawa akeyi a gurin taron maza da mata akan zakkan naira dari biyar, Yau kusan kwanan su biyu ba su komai da shi da ibrahim sai kasafi akan yadda ya kamata sukeyi, Ibrahim yai mamaki kwarai ga yadda ya fahinci cewa Yusuf din yana kokarin ya kawo sallon bada zakkah shi, Ance yawan tambaya ko sa ido yana kowa zubewar mutunci, Don hakane Ibrahim ke yawan yin taka tsantsan ga al,amuran Yusuf daya ke gani, Da marance ya shirya cikin shigar matafiya, inda yadauki jakar shi tankar mai tafiya, Hanyar garin Suleja ya nufa saida yai ta yawo so sai a garin, Inda ya kula da unguwar da yaga talkawa sunyi yawa sosai, Wani massalaci yagani mai irin ginar laka, yadiba da kyau ya dubi yanayin gurin, Komawa yayi yasamu wani hotel yakama don ya kwana, Washegari tun da safe yabar wanan gari na Suleja yaiwa garin kwantagora tsinke, Bayan tafiyar shi waye war gari sai ga jama,a dattawan unguwa sun taru suna, kallon damin kudin da aka aje a, cikin wani katon leda da akai raping din shi ,a cikin massalaci Da farko tsoro sukaji amma daga baya sai akace kodai kudin wani matafiyi ne ya manta dasu a gurin, Sai sukace a kirga sai asamu wanda aka ba ya kai koda banki ne ya aje masu har zuwa lokacin da mai shi zai bullo, su bashi abin shi, Wata yar farar takarda ce tafado daga cikin ledar, da aka fara warwarewa, ZAKKAH A,karubuta da manyar haruffa gabadayan su sai wanan ya kalli wanan wancan ya kalli wancan, gurin yai tsit, Mutun guda daga cikin sune yace ALLAHU AKBAR da karfi sai sauran suka karba mai, a lokaci guda gaba dayan su,,,, Na suka shiga yiwa mai wanan halin adu,an fatan alheri da gamawa da duniya lafiya, A garin kwantagora ma irin haka yadiga rabawa mutane zakka batare da ansan cewa daga gurin shi bane kudin ke zuwa, Jama,a sai zancen ake ta yadawa iri,iri, wasu harda kari sukeyi a,kai cewa, wai ai wani ne kuma sukara yawan kudin da mai shi ya samu, Tunda yaiwa garin shigar dare baya fita ko ina don haka ba kowane yasan cewa yana garin ba, Sai wa yan da yake sallah jam i tare da su a massalaci, suka sani, Yau jumma,a acikin shigar farar shadda dikin tazarce, sai wata fular daya sa wa kan shi mai ruwan Assh colour, Gidan Anty Dije ya nufa musalin sha biyun rana , ba komai ya sa shi ya nufi can ba sai dan ya dauki Assalam su tafi mosque tare, Anty a gida ita daya sai Abubakar tai mamaki kwarai da fa ganshi a lokacin, Baiko kai ga zama ba sai ga yaran sun shigo gida da gudun su don ganin motar uncle Yusuf a kofar gida,, Bayan yagama rungumay yaran dake mai Oyo,yo yadan dago kai yana kallon Anty Dije, Wace ta ke tsaye ta kura mai ido cikin mamaki take kallon shi, Yaushe ka shigo garin nan Yusuf ? Tambaya acikin mamaki take mashi ita shiko sai murmushi yakeyi yana kokarin cirewa Assalam bottiry din rigar shi, Amsa yaba ta a takaice da cewa shigar dare nayi shiyasa, ban fada wakowa cewa zan shigo ba, Dago kai yayi ya kalli Anty yace mata, Sallah Jumma,a nake son mutafi kada mu makara , Daga haka Anty tashiga shiriya Assalam din da,yake jirah, Da sallamar ta tashigo gidan a gajiye don tafiyad ta kawai ya isa ya sanar da mai kallon ta cewa ta gaji, Dakin ta, ta,fada tana kokarin cire, rolling din dake a kanta, A hankali ta sabule abayan da ta aza saman kayan jikin ta, wanda yanzu haka nauyin shi yakai mata ko ina, Cikin shigar da tayi tunda safe, ta,fito, tana sayen da wani shocking material, mai laushi, Cikin kayan da yaya iliya yai mazu ne na sallah,yadin grey colour mai dan adon jan flower, cikin sa da kasan shi, Direct gutin fridge ta nufa don ta dauki ruwan sha, kamshin da taji yasa ta dan dagowa da mamaki Kamar tai magana ko tai tambaya saidai kuma ta shere kawai, Sallah maryam ta gabatar tadan kai wani lokaci a zaune ta lazumi sai ta mike, inda suke aje abinci ta nufa, Abinci ta debo a cikin plate sai kayan garnish din da ta zuba a sama, Zaman ta yai daidai,da shigowar su gidan daga dawo,wa gurin sallah jumma,a Gaban tane ya bada wani , sautin kara don dai gaskiya , A,lokaci guda suka hada ido inda yai sauri kawar da idon shi, Amma zuciyar ta sai wani bugawa yake kamar wace taga abin tsoro, a,lokacin, A hankali ta furta mai kalman sannu da zuwa, ta mai sune kanta kasa,batare da ta kara dagawa ba, Cikin falo ya,shiga tare da Assalam a hannun shi sai carpet din sallah, da ya rika, Sai bayan shigar shi ciki sanan tadan samu sukin fara cin abincin ta , A hankali take cin abinci amma karan plate din ta yana kaiwa a inda suke, Anty Dije wace, ta fito tana kokarin hadawa Yusuf abinci, take,ce wa Maryam, Nasan cewa Baba zai shigo yanzu tunda an sauko daga jumma,a Maryam tace aikuwa tun fada nashigo nake son fada maki cewa, ashe, Wai abokin ya din nan na kan wuri wai yasamu zakkah daga wani bawan Allah, Wanda ba ,a san kowaye ba yai ta bi massalataiya yana bada sadaka saboda Allah da Annabi, Anty Dije tace da, zun fa Almajirin nan ke min labari wai sun tsaya kallon wani mutum ne da ya bude gidan shi sai yaga kudi a kofa cikin ledar an rubuta Zakkah, Yusuf wanda tunda suka fara hira yake sauraron su sai murmushi kawai yayi A lokacin Antyn nashi ta shigo dauke da dan tiren da ta hado mai abinci aciki, Annan take cewa muna can muna maganar wai wani ya tsunci zakkah a kofar shi ashe ma ba mutun guda bane, Masha Allah yace alokacin da yake kokarin bude plate don zuba abinci, Muryan Babane ke gaisawa da Maryam a kofa, Maryam din ke cewa Baba Oyo,yo, cikin tsigar shagwaba, Baba yace ja,ira yau ina diyan naki suke suka barki da taro, But yaran suka fara fitowa da,gudu suna taron Baba wanda ya shigo masu da yar ledar tsaraba, Suna karban ledar suka fara kokarin budewa maryam ce takarba don ta bude masu, Tadan zauna saman gefen simintin su, zaman ta yai daidai da fitowar Yusuf, Har kasa ya tsugun na kamar yadda yaga hausawa na gaida mahaifar su ya gaida Baba, A,a to Bawan Allah ka shigo garin ne, ? Sannu ka kaji ya aiki ya jama,a da kuma ko kari yau da kullun, Allah yai maku albarka kaji, Allah ya taimaka ya rufa Asiri, Ameen Ameen Yusuf ke ta fada kawai, kanshi a duke Ita,ko Maryam sai kokatin bude ledar tsarabar baba takeyi wa yaran daje tsa, tsaye a kanta, Dankali ne soyayye da Awara mai yaji da salad ya sayo masu, kanta aduke tace su dauko plate a sa masu, Alokacin taji muryan Yusuf yana cewa Baba za,a kaika ka dauki photo Ina son bana kashiga cikin masu tafiya zuwa Makkah insha Allah, Da sauri Maryam tadago kai tana kallon shi, sai dai kwarjin shi bai bari ta kai,wani lokaci tana kallon nashi, Baba daje a zaune bai san lokacin da yakai zaune ba a saman dan simintin da Maryam ke zaune gefe, Yaro may kace ? inji Baba, ,, Anty Dije tafito da goro manya farare a cikin leda tana kokarin mikawa baba, Maryam tace, yau baba bazaici goro ba Anty don kin ga ya kasa magana, Da kuwa ya sakar mata yana maicewa karbi nan yan nema, Abinda Yusuf wanda ke kokarin komawa cikin falon ya fada maryam da su Assalam ke fadawa Antyn, Da sauri ta kalli Yusuf tace O, O ni Hadiza, Yusuf ban san may zan saka maka dashi ba wallahi, aduniyar nan, Kafin suyi magana sai muryan baba sukaji kawai yasa kuka wi,wi, Yanata zabga addu,a acikin kukan, Bai iya kara cewa komai ba ya mike kawai yabar gidan, YUSUF yabi bayan shi da sauri tare da jarban goro. A hannun Anty yabishi da shi, Nan yabar su Anty da maryam suna ta famar sadudar maganan, Bai,wani dadewa ba yadawo tare da Assalam wanda ya,bishi da baya, Sai a lokacin Yusuf ya dawo yadan tsaya ta waje yace tare nake son su tafi da, Baba Abdullsamad, Insha Allah, da Ibrahim wanda zai raka su, Ita dai Anty dije sai mamaki zancen kawai takeyi, Ta kalli, yusuf din tace mai wallahi ban san may zance ma ba, gaskiya, Saikuma takama hawaye kawai da dan karfi Yusuf, yace Subbahanallah, Ganin maryam yayi tana goge fuskan ta wanda hakan yasa hankalin shi ya kada tashi, Falo ya koma inda Anty take zaune tana faman share kwallan dake ta faman silalowa daga idon ta, Guri ya samu yana cewa anty haba, haba dai Anty pls ki daina don girman, Allah Yi,wa irin su Baba irin haka tankar taki ne a rayuwar mutum,saboda neman albarka duniya da lahir, ZEEE. MAKAWA [3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Masoya Novel din furen juji tare da sauran yan uwa musulmi na duniya, Ina maku fatan alheri ga wanan safiyar jumma,an da muke a ciki, Ya ubangiji Allah ka sada mu da alherin dake cikkn wanan ranan, Sherin dake cikin ta ya Allah ka kare mu kaimuna tsari daga gare shi, Allah ya karawa Annabi daraja Allah ka kara daukaka musulunci,,,,, 👏👏👏👏👏👏👏 Gaba daya jikin Anty Dije har Baba da maryam yai sanyi saboda jin wanan albishir da Yusuf yai masu na bazata, Anty Dije ta daga kai zuwa kallon inda Yusuf yake zaune tare da Assalam don su ci abinci, Ta, lankwasar da murya tace Yusuf yau na rasa kalar muryan da zanyi ma godiya da shi, Saboda ban san may zan iya furta ma akai ba, al,amarin ka na daban ne Yusuf Shigowar ka cikin mu wani babban alheri ne atare da mu, Gaba daya shigar ka musulunci ta zama ma duk wanda ke rabe dakai alheri, Duk da zamanka Furen kan Juji da farko ban hango wani sheri atare da kai ba sam har izuwa yanzu da kazama wani haske a cikin al,umma, Kafin tai magana sai ya rigata farawa da cewa, batare da ya kalle ta ba,. Narasa albarkan mahaifina na cikina Anty may zai sa bazan bida ga bayin Alkah da suka nuna min kauna ba, Abinda duk nakewa iyayyen mu ina masu ne saboda neman albarka acikin rayuwa, A kullun ina rokon Alkah yasa yan uwana su gane gaskiya su,dawo cikin hanya ma,daidaiciya su ma, Maganar shi taba kowan su tausay da yake fada inda ya ci gaba da cewa, Abinda ke sa ako,da yaushe nake yawan zuwa nan gurin badon komai bane don in cika wani gibi dana rasa nadaga yan uwana, Ànty Dije baki kyamace ni ba tun ina Joseph dina har zuwa yanzu, May zai hana in maki duk wani abinda nasan zai iya saki a farin ciki, A koda yaushe jinku nakeyi tankar yan uwana na ciki daya, saboda irin yadda kike min. Yar kwalar dake shiri silalowa a idon ta tashare, da gefen hannunta, Zaune take a bakin gadon ta tana jin lokacin da a,ke ta kiran sallah la,asar daga makwabtar unguwar su, Amma sai taji yau takasa tashi kamar yadda ta saba yi idan taji kiran sallah, Sai,da taji fitar su shida Assalam sanan tai yunkurin fita, A kofa sukaci karo da Anty Dije, wace ke kokarin shiga gurin maryam din, Suna hada ido da Anty Dije sai ta harare ta ,tace Maryam nikan ban san may Yusuf zai maki wanda har zaki iya mai godiya a duniyar nan ,,, Nadai ga da mama bata da lafiya irin tai makon da yai muna a gidan ñan, Yanzu Maryam agaban ki fa yau yaiwa baba wanan irin alherin da kowani musulmi ke fata, Ina sauraron inji kin mai godiya amma sai naga cewa har boyewa ma kikayi don kada ku hadu, Maryam na in,in niya tace wallahi Anty yanzu nake son in zo in mai godiya amma sai naga yafita, Bata ce mata komai ba banda hararan da ta kara binta dashi , ta juya takoma inda ta fito, Azaton maryam yafitane sai ta fita waje tsakar gida, Da Yusuf suka hada ido yana zaune saman dan dakalin simitin da ke gefe yana alwala, Idan ba idon take mata karya ba wani irin tsadaden murmushi taga ni makale a fuskan shi, Cikin sauri takawar da kanta gefe guda tana mai jin wani nauyin shi, Kamar ta juya takoma ciki alokacin sai dai ta daure kawai ta, nufi hanyar kitchen din su tankar bata gan shi ba, Tunda Yusuf yafita wanan lokacin bai dawo gidan ba sun shiga gari da Assalam da sauran abokai, A cikin shigar kananin kaya yadawo da dare bayan sallah isha,i, tare da Assalam wanda ke dauke da ledar kayan sweet kala,kala, Ko da yai sallama ya shigo maryam tana cikin shigar wasu English wear sun mata kyau so sai, Duk da dare ne mutum zaigane cewa ta gyara fuskan ta tsab da kayan makeup, Ga kamshi dake tashi kamar wace ke sana,ar kayan kamshi, Muryan Ànty Dije ce ke cewa maryam don Allah zo ki tafi hakana kin san halin As,ma,u da saurin rufe gida, Jin muryan Yusuf yana cewa bissimilahi alokacin da zai zauna, Maryam dake tsaye tana kokarun sa, takalma tace mai, "Sannu da dawo wa" A , kasalance yace "Yauwa" Assalam ke cewa little mummy ina zaki zani nima, Kai wani irin son yawo ne haka ? Kadawo ko zama bakayi ba zakace wai zaka, Assalam kai baka gajiya da yawo ne wai, kazauna taje tadawo ko ita dare yayi don dai ina son takarbo min kayan yau ne, Dare ya,yi gaskiya bari mu sauke ta kawai inaga zai fi, Da mamaki maryam tai saurin dagowa don batai tsan,manin haka ba sam Idan son samune ita gaskiya sam bata son shiga motar shi Saboda yana jagula mata hankali duk lokacin da tashiga, " Wai, har hankalina yakwanta inji Anty Dije ta juya gurin maryam tace kin ga ai kin samu sauki Ai yanzu zan dawo da sun zauna kawai, A, lokacin ya mike tsaye yadauki Key's din shi da yazube saman center table, Gadan gadan yanufi kofar fita wahe batare da yai mata magana ba, Ai, da sauri maryam tamara mai baya don gudun masifar Anty, Acikin motar shi yake zaune, tun daga nesa zakaji sautin karatun Al,kur,an mai girma yana tashi suratu Fussilat, Maryam nakara so,wa ta bude motar daniyar shiga, Amma sai batafa Assalam aciki ba shi da yaja mata wanan tafiyar, Da sauri ta kara lekawa cikin motar ko zata ganshi a baya saida baya ciki, Turus tayi tana zazare ido, Sai ta dan ja baya tana dan zare ido kamar mai jin tsoro Ganin har ya kuna motar ya sata saurin shiga jiki ba karfi kamar an zare mata lakka, Ta zauna a hankali tare da cewa ya akayi Assalam bai zo ba kuma, A hankali yafara tafiya batare da yabata amsa ba ya hau saman titi a hankali, Gyaran murya yayi a hankali cikin wani irin soft voice yace aike ce karshen fitowa May yasa baki fito da shi ba ke, ? Maryam wace tasan gatse ne yau mata, ta juya abinta cikin natsuwa, tana kallon fitilon dake a gefen hanya, Sai dai kira,an dake tashi a motar take bi a hankali, Wayar shi ce tai kara alokacin ya dauka yana yar fara,a Sadiya sorry nadan fitane zuwa wani guri sai dai kila bazan dade ba, A hankali ya mika hannun shi yana kokari rage karar sautin dake tashi, Maryam wace taga ya rage saurin tafiyar da yakeyi batasan lokacin da tai yar tsuki mai sauti ba, Sai,dai jin karar tayi yafito fili wanda sam bataso hakan ba ita, Ok to kiti hakkuri tunda ina gari aiko zuwa gobe ne zan shigo, Eh a hanya nake zan kai maryam unguwa ne amma ba dadewa zamuyi ba ai,,, Tuni maryam kan ta yadauki caji saboda jin kiran sunan ta da akayi a zancen Bata karasa jin haushi ba sai,da taji ana cewa maryam ce kuma yau baki sani ba ? Saida su kayi sallama da juna tukun san,nan yadan ci gaba da tukin motar shi, Maryam yace cikin wani murya da zakace dole akasa shi yin magana alokacin, Fuska a daure yace may yasa ki kai muna tsuki, pls,? Wani kululu taji don ai tambayar raini wayo ne wanan Amma a fili sai cewa tayi yaushe ? Murya kasa,kasa irn ta wanda bai son magana da yawa, yace may Sadiya tai maki ki,kai hating din ta dayawa haka, ? Bakaramin kaduwa magana tasa maryam ba, Amma sai taga cewa tai shiru kawai shine daidai, yafi tace zata bada amsa, Maryam pls stop hating me like, dis, Wani abune ya soke ta akirji da ya furta wanan magana Murya na rawa tace ni "Ya Yusuf " ? Kai ya kada mata alamar eh, Cikin kwantar da murya tace, Nashiga uku ta furta a fili, Azuci kuma tace maganar Anty yau ya tabbata ashe ko shi yasan cewa bana son al,amarin shi, Kafin wani lokaci hawayen da suka cika mata ido suka zubo, Are you crying maryam,? Why ? Matsowa yayi gab da ita yana mai mika mata hankici don tagoge fuskan ta, Da sauri maryam tadan ha baya kadan kamar wace taga abin tsoro, Ki yi hankuri pls ban san cewa maganar zatai maki zafi haka ba ? Har da zubar da hawayen ki masu mahin manci, da ma,ana, Cikin hawaye wasu nabin wasu tace may kai min dazan yi hating dinka Bayan yawaita alherin ka a,garemu ko da yau she, Murmushi yayi ya ce gaskiya bana jin dadin the way you are treating me, Haka kawai maryam ta samu kanta da cewa, Insha Allah bazan sake ba Ya Yusuf, Fuska daure yace sam bana son ina batawa mutum rai maryam bansan ko may nake maki ba haka, ? Ki fada min in daina pls, Wani irin nauyi da kunya ya kamata tace, Subbahanallah wallahi ni ba abin da kai min, Ganin sun shigo cikin uguwar da zasune yasa shi cewa ina ne kwanar gidan da zasu tafi ? To ki share fuskanki pls kada ki shiga tagane cewa kinyi kuka pls, ? Ba musu maryam ta goge fuska da wanan kyalen da ya bata, ta goge fuskan ta a hankali, Murya kasa, kasa irin ta mai rada furta, na gode, Shiru maryam tayi batace komai ba, Wani dan iska ya furzar daga bakin shi, Kai maryam ta sadda kasa kawai, A hankali ta bude motar tafita, Binta ya,yi da kallo har ta shige gidan, Sai a lokacin yai yar ajiyar zuciya, Don yaji yarinyar raba shi mugun tausayi sosai, don bai zaci cewa tana da saukin kai haka ba, Saboda yazaci cewa zatai mai rashin kunya idan yai mata magana, Bai wani dadewa ba yaga tafito da wani kumshin kaya, dagani kayan sun mata nauyi tana ja, Da sauri yafito yakama mata yabude bayan mota yasa mata, Komawa tayi zuwa cikin gidan sai,dai wanan karon ta dan dade, Inda ta dawo dawasu kayan again, Sallama taima shi ya dago kan shi ya karba a hankali, Batai magana ba sai kokarin zaman da take yi shiru sukayi a lokacin da yafara tukin motar, Kowa da abinda yake sakawa a zuciyar shi gamay da dan uwa, Wayan shi tai kara inda a zaton maryam take tuhumar ko sadiya ce uwar naci, Amma sai daga baya tagane da Ibrahim yake wayar don kiran sunan Ibrahim din da ya,yi Sai dai da yaren su suke magana inda maryam ke ta mamakin yadda yake yare kamar bashi ba, A falon Anty a,kazube kayan sako ne a ka aiko da su, daga Lagos, Maryam ce ke fadawa Anty ta yadda Assamau tace kudaden kayan suke, Yusuf eanda ke saman dining table yana zuba tuwon semovita da miyar kubewa danya,wanda akaiwa miyar stwee daban yaji, gadan manya,manya Yadda maryam ke bayani acikin sanyi murya ya nuna mai alamar Har yanzu rayuwar ta ajagule yake da zancen su, Tun da har taki sake jikin ta har zuwa yanzu, Kudin kowani kaya take fadawa antyn ta a hankali tana taya ta dubawa Abincin shi yake ci a hankali kamar hankalishi baya gurin su, Wayan maryam ce yai kara taciro shi daga cikin poss din ta, A yadda take magana ko antyn ta dake kusa da ita bawai lalai, ne taji ta ba, Mikewa tayi zuwa cikin dakin ta, karba wayan ta, dake a hannun ta, Amma, wanda ke falo zai iya jin maryan ta,kamar tana waya har yanzu, Sama sama tadunga jin muryan su don yakai wani lokaci agidan yana mata hiran kakar shi, Sai yanzu,ne mutanenn gari suka gane cewa ya shigo garin, Saboda duk kwana kin da, yayi agarin acikin gidan shi yake zaune, bai fita ba don gudu kada a rushe mashi plan din shi, Wayar shi tai kaa alokacin da yake tuki motar zuwa gidan shi, MY DAD Yagani a rubuce yasan a kwai abinda ya faru ke nan tunda Dad yau yakirashi, Ya dauka da cewa Alo, Bai ansa mai ba sai magana cikin fada,fada ya keyiwa dan nashi, Yace suna son kudin church don an,kawo masu sabon pastor , YUSUF yai mamaki kwarai da jin maganar mahaifin don alama ya nuna cewa har yanzu bawai ya saduda bane ke nan akan zancen shi, Har yanzu yana mai kallon Christian ke nan ashe, ? Dad iam not in your religion now, So don't involved me in any church matters again pls, Sai kuma ya juya da harshen su na ibo yace indai shi yake bukatar kudi kowani abu zai iya bashi a tsakanin su , Mr Ema wanda sam bai yi tsan mani Yusuf zai iya rufe ido yai mai haka ba, Ahankali yadafa, kujerar da yake tsaye gefen ta yakai zaune, Yana mai jin wani irin kunar zuciya atare dashi, lokacin, Kwallar masu zafi ya matse daga idon shi saboda ya san cewa ya yi loosing din Yusuf ke nan har abada, Shiko yusuf daga inda yake ya rintse idon shi saboda baiji dadin yadda sukayi da Dad din ba sam, Amma yasan cewa hakan shine kadai hanyar da ta dace ya daina Dangantashi da akidar church, Maimakon yaje gida sai ya wuce gurin Abdulsamad yafada mai yadda sukayi da mahaifin nashi, Abdulsamad yace mai, ai da yabashi kudin kawai amatsayin kyauta idan yakai masu su suka sani, Yace kasan cewa duk lokacin da zasuyi canjin pastor kashin kudi yazo kenan, Shawarar Abdulsamad yabi inda yaturo mai dubu dari biyu chur washegari, Shikuma yadauka yakai, church yace ga gudun mawar yusuf nan, Aisai murna da shewa suna wakoki cewwa yusuf zaidawo soon, ZEEE. MAKAWA [3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: .🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Assalamu Alaikum yan uwa musulumai masoya novel din furen juji, Nuna kaunar ga novel din shine taimakon kara min karfi cigaba daga gare ku, Shawaran ku agare ni tankar taki ne mai kara min karfin hafbaka da cigaba Nagode Nagode Nagode kwarai daga gaske 👏👏 Wasa wasa zancen Sadiya da Yusuf sai kara ci gaba yake yi, Yanzu haka kokarin hada kayan mungani muna so Da kuma kayan azumi da na sallah sukeyi, shida Anty Dije da Jibrin, Yau ma kamar kulun a waya,suke zancen wasu materials da ya turo Ibrahim ya kawo mata, a sa acikin kayan, Ganin kayan da kuma tsadan su yasa Anty Dije cewa Yusuf wa yan nan kayan ai sai a cikin lefe ko,? Maryam wace ke sawa Abubakar Pampers, alokacin ta ce a to ku dai yi ta sawa in hau,kane abin, Anty Dije ta manta cewa waya take yi sai tace wa maryam, Abinda mutun ke so maryam a maida shi yake yi tankar kwai, Dariya Yusuf ya yi daga cikin wayar yace Maryam ce ko ? Anty ta bashi amsa da cewa itace ma na, Yar bakar magana,wai muna sa kaya kamar bamu tunane, Dariya yakarayi Ya ce Anty Ta karba mai yace don Allah duk kayan da Ibrahim yazo da shi jiya kiba maryan su pls, What's, Tafadi da karfin Allah ,har hankalin maryam ya dawo gurin ta da sauri ta dago tana kallon yar ta, Lokaci daya maryam ta juyo tana fuskantar Anty nata, zuciyar ta tab da tambaya, Ji tayi Anty nacewa Yusuf ban fahinci kalman abarwa Maryam kayan ba ? Cikin wani irin razana Maryam tace wa Anty saboda may, ? Sai kuma ta dukar da kanta kasa ta na mai jin kunar ran abin da anty tai mata, Don may za suyi magana a tsakani su har anty ta daga murya Yusuf yaji su, Tana gama sawa yaron Pampers din tamike tsam tabar gurin cikin kunar rai, Da harara anty Dije ta raka ta har tabace mata dagani, Kwance take rigingine fuskan ta na kallon silin din dakin , Sai,dai idon dake tab da hawaye, A hankali tazauna bakin gadon tana kallon ta cikin jin takaicin irin halin maryam akan Yusuf, Karan ledar kayan ne maryam taji yata dan dago kai, Zaune tai kokarin tashi cikin mamaki take kallon yar uwar ta, ? Mika mata tayi tana cewa Yusuf yace abar maki wanan kayan a matsayin kayan sallah ki namu in zai zo, zai zo da su, Maryam wace ta bude baki da zumar yin magana sai Anty ta daga mata hannu alamar bata son jin komai, Tace yai min bayanin cewa kayan sunyi yawa amfada mashi cewa sai za,a kai lefe ake kaiwa da yawa, Don haka tun wutowar Ibrahim bayan Jibrin ya fada mai shine yai shawaran cewa bari yabar maki a matsayin kayan sallah ki, Tunda wai rin su Jibrin ya sayawa safiyar shi don haka sai kuyi anko, Bata san lokacin da tai yar ajiyar zuciya ba, don ta fahinci cewa ba fushi yayi ba ke nan, Anty ta mike tsaye tana cewa sai ki daina fushi, ki, kirashi dai ki masa godiya don nasan halin ki, da basarwa, A hankali tace to don har yan zu ba, wai ta gama sakewa bane gaba daya, Batai saurin kiran shi ba kamar yadda batai saurin bude ledar kayan ba Kayan suna aje a,gefe guda cikin ledar da akawo su, Har zuwa yanzu maryam bazata iya cewa ga kalan kayan ba don bata diba ba ko, a,lokacin da Anty Dije take kokarin budewa dazu, Saida ta tab batar da taga komai don haka ta tuna da ledar don ganin shi da tayi a gefen gado,ajiye, Ledar ta jawo tafara zaro kayan a hankali, saida ta mike tsaye don ganin irin kayan dake ciki, Materials ne da Swiss masu tsada har guda biyar a cikin leda kala masu kyau da daukar ido, Kudin kayan zai kai kusan dubu dari uku da hayi, Cikkn mamaki ta nufo waje inda Anty take tana goge kayan kitchen din su, Anty kin ko ga kayan dake cikin ledan nan kuwa ? Sai da ta juyu suna fuskantar juna take ce mata nagani maryam a shi yabani mamaki wallahi, Ki diba fa yadda mutum zai maka,wanan irin alherin a lokaci guda, Ni wallahi halin Yusuf tsoro yake bani mutun bai jin zafin kashe dukiyar shi haka, Shin kin ma kuwa kira shi kun mai godiya maryam, ? Wani irin kunya ya lulube maryam agurin cikin jin nauyi ta dukar da kanta tace ,a,a Amma ko halinki sai ke maryam ban san wanan halin naki ko ina ki ka dauko shi ba wallahi Ga baba nan ya ta yawon fadae alherin da akai mai ko ina ama ke irin wanan kyautar haka kin kasa kiran mutum ki masa godiya haba dai, haba Maryam, Tsaki taja ta juya wa maryam din baya taci gaba da aikin ta, A masife tana cewa idan kin ga dama kada ki kirashi ma maryam, Haka tajuya takoma daki rungumay da kaya a hannun ta, Wanka tashiga tagyara jikin ta tsab tai sallah shafa,i da wuturi, tadan kai zuwa tara da wani abu zaune saman sallayan ta, Ta mike tsam zuwa bakin gadon ta da yasha gyara kamar ba a sama za,a kwanta ba, Zauna wa tayi a hankali ta mika hannu ta ciro wayan ta saje makale yana caji, Nobar Yusuf ne ta nema takai wani lokaci ta kurawa sunan ido ita kuma bata kira ba, Can dai ta daure ta latsa nobar a hankali tare da gyara zaman ta, da kyau, Yadawo agajiye don har dare yana office yau saboda kayan su da yashigo daga Korea, Wanka yashiga saboda bai sha,awan cin komai ruwan tea kawai yake ra,ayi yau din Dan karamin towel ya sa yana tsane run dake a kan,shi Wayar shi ce yaji tai kiran Sallah alamar kiran ya shigo mai, A hankali ya isa gurin da ya jona ta acaji ya ciro ta alokacin har ta kusa katsewa ko, Maryam KG a karubuta a jikin sunan dake kiran nashi, Furta sunan yayi a fili ya ce Maryam a hankali, kamar ta kusa, Jira yayi kiran ya katse sai ya kirata, da kan shi don kada ya ci mata kudi, Tana kokarin kiran shi taji kiranshi yashigo a wayar ta, Bayan ta dauka sai kuma tai shiru a nata bangaren tana sauraren shi, Shi ma dai shirun yayi a lokacin don yaji sallamar ta tunda ita tafara kiran shi, Jin shirun da sukayi yai masu dan yawa ne yasa su yin magana alokaci guda, Assalamu alaikum yace ita kuma tana cewa hello, duk alokaci guda, Murmushi yayi wanda taji a nata bangaren kamar a fili yayi shi, Ina wuni ta kara furtawa a cikin zakakan muryan ta mai kama da busa, Kwaikwayon tayi da cewa lafia kalau, kamar yadda tai magana, Kafin tai magana sai ce mata yayi matar lecturer halan yau ya cika maki waya da kudi ne dai, Don naga yau an,kirani kai tsaye, Murmushi kawai tayi don ta san cewa tsokana ce kawi yake mata, Katse shi ta da cewa Ya Yusuf sai kuma naga kaya wai kace abani, Ya ce eh maryam don dake naga kayan sun dace shiyasa nace kawai abar maki kuyi anko da budurwar Jibrin Shiru tayi kamar baza tai magana ba sai kuma ta tuna cewa yin maganar ta zai jawo mata fada gurin Anty, Sai kawi tace to nagode ya Yusuf amma dai da naga kamar doguwar budurwar ka ka sayawa su, Wani irin malalacin dariya yayi yace sai kuma ga rashin da,cewar su da ita Sai da yar budurwar mr lecturer suka dace kawai shi yasa na ce abarwa matan malam su tayi wa malam kwalliya yasha kallo Ko yar kauna ta ? Wani irin abu taji ya tokare ta a zuciya Tace to zuciyar ta yana nufin cewa A, A ba zai iya saya min bane ko may ? Kawai sai taji tamayar mai da kayan shi tace batason ta gode kawai,ya bar su, Amma sai taji muryan shi a cikin sasautawa ya na cewa maryam, Kayan sallah ki na aiko maki da su saboda kayan da na sayawa sadiya naji ance sunyi waya Shi yasa nace wa Anty tabawa little sister dina kayan ta na sallah su,kuma idan zan zo zan shigo masu da nasu, Kinga saura shoes da bags ke nan ko ? Kamar ya,na ganin ta takada mai kai alamar eh, Yace size din ki zaki fada mun kin ga zai fi idan kuma da akwai wani abin kina iya fada min sai a hado maki da shi, Kwata kwata maryam bata so wani abu daga gurin Yusuf ba , Amma ya ta iya tun da gashi ya,dage har da cewa yasan , Ya,san bai isa sai mata abu ba saboda tana da dubun su To amma yanzu tunda sun shirya yana son ta nuna mai cewa ta hucu kabar kayan zai nuna mai alaman hakan Tambayar ta yakara yi in akwai wani abin da zai sayo mata in zai zo, Ba komai ta furta a,hankali kamar mai shirin yin kuka a lokacin, Sai yaji tabashi wani irin tausayi irin yadda tai mai magana a cikin damuwa,,, A hankali tai mai sai da safe ta kashe wayan ta ba tare da ta kara furta wani kalma ba, a,kai ba, ta,katse wayar, Lumshe idon shi yayi alokacin kamar mai jin barci tare da fadawa saman gado ta baya,, Haka ya kwana da tausayin maryam a cikin ran shi wanda bai san dalilin hakan ba Ita ko maryam ba yadda ta iya saboda har taji Anty na fadar irin dinkin da za taiwa kayan, Sosai alakar mai nisa ta shiga tsakanin Ibrahim da Ejoma wace yanzu duk suna zaune a gidan yusuf ne dakw garin Abuja, a karkashin kulawar shi, Tun suna kojarin boyewa maigidan nasu Yusuf har takai yanzu basu iya boyewa, Maman choima da fara ganewa taiwa Ejoma magana acikin ka ,kausar murya cewa ta rabu da Ibrahim din tun Yusuf bai sani ba, Amma sai Ejoman tace ma mama ai tafi son yasa don ya yanke masu hukunci, Ran yar tsohuwar bai yi dadi ba sai tafito fili tacewa Ejoma ya zatayi da addin ta idan ta aure shi, Sai da Ejoma tai yar dariya san nan tacewa mama ai su addinin su bai hana su auren yan addinin mu ba, Sai,dai matan su ne ba,a yarda su auri mazajen mu ba sam, Ehye, u see Inji mama tana mai kada kai tace tana mai ba Ejoma shawarar ta tsaya a ,addinin xa iyayyen ta suka haife ta aciki yafi mata, Ganin cewa ba,zata iya shawo kan yarinyar ba yasa ta kawar da kanta gefe guda, Tsayin wani lokaci babu wanda yace wa dan uwa kala a cikin su Don dai ita Ejoma gaskiya zata iya rabuwa da addinin ta tunda dama tadade tana sha,awar musulunci, Yin Sallah da sa hijab na burge ta sosai, a rayuwar ta, Har zuwa lokacin dawowar Yusuf da Ibrahim yayi daga office suna zaune a hakan, Ibrahim wanda ya fara shigowa dauke da yar brief case din Yusuf a hannun shi, Ya gaida mama acikin ladabi amma fafir yar tsohuwar taba shi baya taki karba mai sam, Yana tsaye yana mai mamakin abin da yahana ta karbawa Yusuf yashigo cikin gidan, Cikin irin takon shi na alfarma ya Wanan tafiyar tashi, guda guda tankar yana tsoron kasa, Suit ne ajikin shi mai ruwan asshh, colour, hade da wandon shi sai far tie shirt da yasa daga ciki, Isowar shi falon ne yaji muryan Ibrahim yana cewa mama idan har yai mata ba daidai ba ta yafe mai pls, Da mamaki Yusuf wanda yadawo a gajiye ya tsaya yana kallon tare da tambayar ko may ke faruwa, Kafin Ibrahim yai magana mamace tafara magana acikin fada tana cewa Yusuf ya maida ita gida tunda taga kowan su yana musulunta Gaskita ita bazata yarda azo da tsufan ta a cuce ta, Da mamaki Yusuf ya juya inda Ibrahim yake. tsaye don karin haske, ga maganar, Kafin wani yace wani abin Ejoma tafi daga ciki tana cewa , Brother zan koma ga addinin ku saboda wanda nake tare da shi yanzu dan addinin ku ne , Cikin mamaki Yusuf ke kallon Ejoma wace ke mai bayani a lokacim, Cikin mamaki yake nunata da yatsar shi ya na cewa Ejoma ke, ke, ke, Yace nasani sani cewa warana zaki gane hanyar gaskiya insha Allah, Gashiko yau da kanki kin dawo saboda ra,ayin ki, Baki sake da mamaki mama ke kallon su duk ta kawo iya wuya, saboda haushi, Ciki tashige tana ta faman fada kamar wace akaiwa wani abu Karin bayani sosai Ejoma keyi mashi ta yadda zai fahince ta Sai ga mama da jakar kayan ta tana ta fada cewa wai a kwai evil din dake cutar su agurin, Da kyat Yusuf ya samu takoma don ko shi saida yace mata akwai yan rituals a waje sanan ta yarda ta koma, Tafiya take cikin sauri saboda tana son komawa gida da wuri yau, Gurin bus stop take kokarin zuwa kozata samu motar da zai kai ta cikin gari da wuri, Horn taji anayi a bayan ta batare da ta waiga don ganin mai shi ba don bata tsan mani cewa ita akewa horn din ba, Saida, taji muryan shi yana cewa Maryam bakya ji ne halan, Sai a lokacin maryam ta juya ta san cewa da ita yake, A hankali ya samu guri ya Parker motar shi kamar ta wuce sai dai ta daure kawai ta nufi gurin shi, A hankali ta gaishe shi cikin girmamawa kamar kullun, Ya amsa mata acikin husky voice din shi Yatare ta da cewa maryam wai guduna kikeyi ne yanzu ko may, Don yanzu sai ki shigo cikin school din nan batare da kin je guri na ba, May nai maki halan kike min wanan judgment din pls,? Daidai lokacin da ta bude motar tashi ga ta zauna da kyau tadan kalle shi da dauraren fuska tace, Haka dai kagani malam amma ni may zai sa in ma haka kawai, Motar yaja suka bar gurin tare da ci gaba da lalashin ta, Nan yake sheda matacewa yasan ta na fushi dashi don tana gani kamar yaki maida hankali ne a kan zancen su, Yace ya turawa mahaifiyar shi da wani kawun shi don yaje akai karshen zance, Maryam dai batace mai komai ba banda cewa da tayi Allah ya kyauta kawai. A kofar gidan su ya aje ta tare da kara bata hakkurin cewa insha Allah komai zai zama daidai, Sai a lokavin maryam tadan sauko daga fushin da tayi dashi saboda yana yawan sa mahaifinta na fada da ita da Anty cewa sun mai dashi bi nan, Rana akeyi ga kuma alamar hadari da ya rufe ko ina giragizai suna yawo alamar ruwa zai iya zuwa ranan, Tasamu Anty ta rage duk wani aiki da zasuyi a yinin ranan, Tana zaune tana kallon tv ita da Abubakar wanda ke ta wasan shi shi kadai, a tsakar falon su, A gajiye ta fada saman kujera tana mai cewa wayyo Allah na wash , Har kun dawo inji Anty tana kokarin mikewa tadauki Abubakar din ita maryam, Ganin yadda take fara,a yau batare da tashige watsa ruwa kamar yadda tasaba ba indan ta dawo yasa Anty gane cewa tana cikin farin ciki yau din, Tambayar ta yi dacewa halal A, A ya sauke ki naji horn din motar shi, ? Maryam wace ta dan dakatar da wasan da takewa yaton don jin tambayar da yar ta tai mata, A hankali tare da sauke yaron dake hannun nata ta amsa da fadin cewa eh a hankali, Nan take fuskan Anty ya canza ta nuna wa maryam din bacin ranta sosai, Nan ta shiga yi mata fada akan cewa gaskiya ita zata fadawa baba don yafidda ita daga cikin wa yan da yake zargi, Maryan cikin marairaicewar murya tace anty kwanan nan zai turo Insha Allah, Harara anty ta watsa mata irin na ke kika sani din nan,,,, ZEEE MAKAWA [3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Jin,jina gare ku ko yau yan uwa masoya novel din furen juji, Tsayawa rubuta sunan ku zai ci muna time shiya sa nake rubutawa a jam,i gabadaya, Nagode kwarai da irin kainar da kuke gwada min har kullun, Allah ubangiji ya karawa,Annabi daraja Allah ka,taimaki musulmi duk inda yake,👏👏👏 Dole yatafi garin kwantagora ya samu Abdulsamad akan zancen Ibrahim da Ejoma, Don haka yafara shiri matsalar shiguda yanzu shine yadda zai yi handling din maman Choima, Idan son samu ne cikin wanan week din ya shiga garin, Sai dai kuma ga aiki yai mai yawa,sosai yanzu da wuya yasamu zuwa cikin,wanan satin, Zaune yake ya mai,da hankalin shi ga computer shi inda yake ta shigar da wasu sakon,nen masu mahinmanci, Wayar shi ce tai kara ya mika hannu guda a hankali ya dauko wayar dake aje saman tebur din nashi gefe guda, Jibrin KG yaga an,rubuta saida yadan sake murmushi yace ya dai man ? Yace wallahi tun dazu naso inzo office din ka amma aiki ya hanani yau muna entered din kayan da suka shigo cikin wanan satin, Sai kuma Jibrin din ya canza topic da cewa ga kuma tafiya ta, taso muna, Kaida wa in ji Yusuf yake tambayar Jibrin din ? Sai da Jibrin yai yar dariya sanan yace dakai mana , Tunda shi KB dama already yana can tun jiya, Yusuf tace look Jibrin ina son shiga KG so,sai amma aiyuka sun min yawa , Dole sai zuwa satin sama koda zan tafi din yanzu, Jibrin yace zancen baby din nan ce na gurina ya taso shine suka kirani wai inzo zasu sa lokaci, Yusuf yace wa safiya ? Ya amsa da cewa ita fa, kaga zamu iya zuwa mu ga su uncle di na akan zance Sadiya dayani Don ina ga haka zai fi muna sauki da zuwan da zamuyi har sau biyu a cikin lokaci guda, Shiru yayi kamar mai nazari wani abu yana sauraron Jibrin din, Ko ya kagani ne man ? Jibrin ya,tambayi Yusuf din Don haka bayan kwana biyu suka shirya zuwa garin kwantagora , Mota uku kawai sukai tafiya da su wanan karon basu zo da mutane da yawa ba, Badon komai ba sai ganin dayayi cewa yanzu an rage kawo mai hari daga church din su, Sai da suka kusa kawo wa sanan Yusuf yabugowa anty Dije waya yana sanar da ita cewa zai shigo gari yau insha Allah, Idan har yana cikin mota yafi bukatar yai tukin mota da kan shi Gashi kuma da masifar gudu a saman titi sai hankali wanda ke ciki, tare da shi ya tashi,,, Shikan shi Jibrin yana mamakin yawan shakuwar Yusuf da Anty Dije, Tunda yaga suna shiga gari, ya karya kwanar unguwar su Anty Dijen, Saida Jibrin ya kasa daurewa yace wai man nifa har mamakin, kake bani, Saida yadan juya inda jibrin yake zaune yace namay fa,? Dariya kuma jibrin din yasa alokacin yana ta girgiza kan shi kawai, Cak ya tsaya a kofar gidan misalan karfe biyar na yamma, Yan samarin dake zama gefen gidan duk yamma suka yo kansu gaba dayan su, cikin murna, Saboda sun san cewa zasu samu abin tabawa ke nan, Hannu ya mika masu gaba dayan su a cikkn sakin fuska suke ta gaisawa da su, Wani wanda ya samu kariya a sanadiyar hatsarin mashi yana kokarin taso wa zuwa gurin shi, Da sauri Yusuf ya nufi inda yake yana cewa malam Aliyu har yanzu kafar nan tana nan ashe, ? Bayan sundan yi ban hannun sun gaisa matashi wanda Yusuf yakira da malam Ali ya ce ma Yusuf, Wallahi gani nan dai yanzu wai asibitin kashi na kano nake son zuwa a diba min ita, Sai,dai kuma abin tafiyar ne sai a hankali wallahi, Yusuf yace haba, haba dai ai da sai muyi waya ko, Bari zan gan ka idan na huta ai yanzu shigowar tamu ke nan, Maryam ce tafito daniyar zuwa nan yar kasuwar bayan kwanar kuka don ta sayo yan abubuwan da suke bukata don yin abinci dashi tunda yace yau zai shigo, Turus taja tai tsaye don ganin da tai masu akofar gida, Cikin kasa boye mamakin ta take kallon su Harara ya saki mata daga inda yake a tsaye yace shine taron da za mu samu ke nan ko, ? A hankali yake kokarin takowa zuwa cikin gidan nasu, Gefe maryam ta dan rabe mai don yashige,amma sai yadan kurawa maryam ido wace a ko yaushe cikin kara canza mai take, Ya na zowa daidai inda take tsaye yasa kafar shi ya take mata yan yatsun kafar ta da takalmin shi, Wani irin dan sautin kara, ta sake, a lokacin guda da sauri ta daga kai ta dube shi, Amma sai taga bai ma ko kallon inda take, sai kokarin gyaran kwalar rigar shi yakeyi, Murya na rawa tace wayyo ya Yusuf katake min kafa fa, Har zuwa wanan lokacin bai nuna yaji may tace ba, Sai wani irin zugu take ji a yan ya tsun ta,gashi sai kara matse mata su yake da takalman shi, Zafi da radadi ke ratsa ta alokacin gashi shi yaki daga kai ya kalli ko da gefen da take tsaye ne, Wasu hawaye masu dumi suka silalo daga idanun ta, Takara cewa dan girman Allah ya Yusuf kayi hakuri, Sai a lokacin dan sasauta mata kadan wani irn ajiyar zuciya ta sake cikin kuka, Sai da ya hango Jibrin yanufo kofar shigowa gidan yai sauri yadan ja baya kadan, Yantsun kafar nata, ta kalla sunyi wani irin ja jajir A hankali ta dafa bangon dake gefen ta, tana bi a hankali cikin dan gyashi, Nan da nan ya tsuke fuskan shi kamar bashi bane yai mun wanan muguntar, A lokacin jibrin ya karaso gurin yana cewa an sauke kayan ga mutanen ka nan zasu shigo dashi, yana nufin samarin nan da ke kofar gida, Sai a lokacin idon shi ya kai ga maryam wace ke kwalla, wahala, What's going on here man,? Tankar da dutse yake magana yake magana don ko kallon shi bai yi ba, Kokarin wuce jibrin dake son jin abin dake faruwa ya yi, Sai a lokacin maryam tace mugu kawai azzalu,,,,,, Saboda yadda ya waigo ta rai a bace idon nan sun kada sun yi mai jajir Matsowa yayi a hankali batare da yadamu da jibrin na gurin ba ya dan nuna ta da yar ya,tsar shi ya ce Ki kiyayeni fa don bata maki tsari, Bata son nuna kariya a gaban shi don haka sai ta dake acikin tsiwa itama tace mai In dan ban ki yaye ka ba fa sai may? Kai ya gyada mata yace ok haka kikace ko ? Zaki san kin taba Yusuf maryam, Ya wuce fuuu ciki yabar ta nan tsaye tana kara kallon yadda kafar ta yai wani jajir a lokaci guda, Wani hawayen takai ci ya kara zubu mata a fuska ta sa gefen hannun ta takara sharewa, Sai a lokacin ta sauke wata irin ajiyar zuciya wanda bata masan tayi ba, Amma zuciyar cushe da mamaki da tambayar abinda taiwa yusuf yai mata wanan salon muguntar, Da murna Anty Dije ta tare shi tana kuma yi mai korafi cikin harara, A she saida kaga cewa zaka shigo gari shine ka kirani, ko,? Yai yar dariya ya sosa kan shi da key din dake hannun shi, Ai don kada in kara laifi nai ya sa na bugo maki lokacin muna bayan mariga kadan, Kai Yusuf karage wanan gudun wallahi, mutun baya tausayin kan shi, Shigowar jibrin ya sa tai shiru nan suka fara irin ba,an da akeyi a tsakanin matar wa da kanin miji, Falo Yusuf yashiga ya zauna ya bar su nan suna ta shan matar juna a tsakanin su Shigowar maryam yayi daidai da isowar ta da ruwa a cikin gora taba Jibrin Batare da anty ta kalli fuskan maryam ba tace maryam ba Yusuf ruwa don Allah, Jibrin yai sallama da su yana cewa zai tafi ya kai tsara ban da yayo gida don kada zafin buth ya lalata su, Zaune yake saman kujera amma zaman balance yayi alamar yana tare da gajiya alokacin, Tashigo falon batare da sallamar ba, duk kan shi na sama idon shi a lumshe bai hana yagane cewa ta gurin ba, Saboda kamshin da ya daki hancin shi na turaren ta duk a ranan humrah kawai tadan shafa, A hankalo ya bude idon shi ya sauke su gare ta, gutun hawayen dake makale a fuskan ta yai tozali dasu, Subbahanallahi ya furta da sauri har saida maryam din tadan razana Tana waigen bayanta ko wani abu yagani yake kiran suna Allah maigirma haka, Cikin wata irin murya ya fara magana, Dan Allah maryam kiyi hakkuri ki yafe min pls, ban san cewa zaki ji zafi haka ba har ki kuka, Banza tayi da sai ta dangwar da tiren da takawo mai abin shan açiki gaban shi, Tana kokarin mikewa yai yunkurin kai hannun shi da niyar ya rike ta, Komay ya tuna kuma yai sauri ya jaye hannayen shi gare ta, A,rau,nane yakara fadin don Allah dai maryam kiyi hakuri Wallahi wasa nake maki saboda naga baki tare mu ba kina muna kallon mamaki, kawai, shine nataka maki kafa don ki san ba mafarki kikeyi ba, Kala maryam batace mai ba sai mikewa da tayi tana kokarin barin gurin, Haba maryam ina mun daina fada dake haka don may zan baki hakkuri ki kyale, ni,? Ganin zai sa har anty taji ta dauka ko wani abin ne yasa maryam, Tai saurin dagawa daidai lokacin da shima yadago sai jikin su ya gogi juna Cikin sauri tabar falon batare da ta ko waiwayo inda yake tsaye ba, Sai da yaga shigewar ta ya karkada kan shi yana murmushi don dariya ma ta bashi, Sai gab da magrib ya bar gidan zuwa gidan shi don yaje ya watsa ruwa, Washegari zaune suke saman wani benci a kofar gidan Abdulsamad din, Cikin yaren su suke magana , Abdulsamad din ne bayan ya gama jin bayani Yusuf a kan zancen Ibrahim da Ejoma, Yadan gyara yace wa Yusuf aiko don yariyar ta musulunta bazan hana Ibrahim auren ta ba sam , Ba don komai ba sai don jahadin da zai yi, ceto rayuwar yarinyar da ga kafurci, Kai Yusuf ya kada don ya kasa ban,banta sakanin shi da Abdulsamad wanda ya rike musulunci gam gam gam tankar addinin da aka haife shi a ciki, Abdulsamad din ne ke bashi shawaran cewa idan yazo yadinga zuwa yana gaisawa da mahaifin shi tunda yafara saukowa, Yusuf wanda dama yana da niyar yin hakan amma kuma sai yaji dadi da shawaran da aka kara bashi akai, Yaji dadi sosai na rashi samun matsala akan zancen Ibrahim din da Ejoma wanda dama bai tsamani haka din ba daga dattijon, Sun shirya cewa azo da ita nan kwantagora a musuluntar da ita zai fi don mutane su sheda musuluntar nata, Daya tashi wani katon shago ya shiga yai wa mahaifin shi sayayya a ciki sai daga ciki babu abin maye sam, Direct gidan su ya wuce don yasan cewa yanzu suna gida basu fita ba tukun, Taron da ya samu yau ba yabo ba fallasa a kai sai dai shi bawai yadamu bane da yadda ake wani daure mai Tunda yasan cewa ba wai laifi yayi ga Allah ba akai, Sun danyi hira da mahaifin saidai duk akan viwon shi ida Yusuf din yake cewa zai zo ya kai shi asibitin Turkish da ke abuja don adiba shi, Ga mamakin shi sai yaji mahaifin nashi bai yi musu ba akai, sabanin yadda ya zata zai ce bazai tafi ba, Karshe Mr Ema din yake cewa Yusuf yana son wanan Christmas din yazo gida ayi da shi, YUSUF bai musa ba sai cew yayi in sha Allah zai zo a lokacin, Dan dattijo ya bata fuska shi jin, dan ,nashi yace Insha Allah acikin maganar shi, Daga gurin mahaifin shi ya juyo zuwa gidan Anty Dije don ya yi breakfast, Duk da yake a gidan mahaifin nashi yasa may su, suna batun yin break, Maryam bata gida yau tunda safe ta tafi gidan su SAFIYA, Ba don komai tayi shawaran zuwa wanan uguwar ba don kawai gujewa haduwa da Yusuf din wanda ke gari, Tun safe sai dare zuwa bayan isha,i ta dawo daga u,subu can uguwar su safiya din, Da yar fara,ar ta ta dawo tunda tana zaton ya,tafi ko tunda da Jibrin suka zo garin don haka tana zaton suna tare Amma sai fara,ar ta ya lake lokacin da taji wanda ya ansa mata sallamarta, "Sannu da dawo" Abinda ya furta mata ke na, A cikin matse fuska ta ansa mai da "Yauwa" Wani murmushi yayi kama da yake, duk da dare ne sai da maryam tagane na mugunta ne, Yau kuma unguwa aka tafi har dare haka,? Kafin ta san ansar bashi sai taji duk ta dabur ce, Harara ta sakar ma sa ta gefen ido tace, Ko a kwai wanda zan wa aiki ne idan nadawo da guri, Maryam ta shige dakin ta tana kokarin cire hijab din ta, amma ta tuna nen ina Anty taje cikin daren nan, Don bata ji motsin ta a gidan ba, Falon tadawo don ta diba dakin Anty tagani ko lafiya, A hankali ya tako, har zuwa inda take tsaye kofar anty Yana saye da kananan kaya sun karbe shi sun mashi mugun kyau, Duk da a cikin dare ne kyalin agogon hannun shi ya wadatar da maigani yasan cewa gold ne, Ganin shi yanufo inda take yasa ta saurin dan ja da baya kadan, Gurin fridge yanufa yadauko ruwa a gora tare da hadawa cup din dake saman fridge din, Baki da gaskiya ne kila ko yace a hankali, sai dai fuskan shi daure tamau, Batare da tai magana ba ta kara danna mai harara, tace, I don't want to talks more with you, B/couse of your wickedness, So please excuse me ta fada cikin murguda baki, ganin yayo kanta gadan gadan yasa ta saurin shigewa ciki da sauri, Muryan Anty Dije ne ke cewa wai har yanzu maryam bata dawo ba ne ? Kai ma da kan ka kake service din kan ka yau, maryam tana ina, Kamar ba shi ba yace ina ga kamar sallah takeyi,, Maryan dakejin ya kare ta tai mamaki sosai a,cikin zuciyar ta, Kamar ba shi bane Yusuf Joseph wanda ta sani a da, Mai daurewa bai magana bai dariya bai shi ga harkan kowa, Kodai shigar shi musulunci ce ta sauya mai rayuwan shi Muryan Anty ce ke kiran maryam din ciki daga murya, Take gabanta ya fadi don tana gudun tai mata fada gaban Yusuf, Sannu Anty da dawo tace adan daburce kamar mara gaskiya, Haba maryam ga Yusuf zaune kin ki fitowa kiyi serving din shi sai da ya tashi da kan shi, Cikin kwantar da murya tace, Na zata ba yanzu zai ci ba ai shiya sa ban fito ba na tsaya yin sallah, Ke dai kan halin ki sai ke maryam haba yaushe zakibar bawan Allah azaune yana jiran abinci, Daga haka batakara cewa komai ba itama maryam din ciki ta koma abinta, Sai da ya gama takira maryam tace tazo ta kwashe kayan, Murya kasa kasa ta yadda ba kowane zai ji abin da yace ba Next time zaki yi bayani ai , ZEEE. MAKAWA [3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣6⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Ya Allah ka kara muna imani da tsoron ka azukatan mu Ya Allah kabu ikon bauta, maka bauta mai tsariki a cikin aiyu kan mu, Allah ka karawa Annabi dara da daukaka, Allah kataimaki musuluni karufa mai asiri duk inda musulmi yake a duniya👏👏👏 Ejoma da Ibrahim sun iso kamar yadda Abdulsamad ya buka ta dacewa su zo, A gidan Ànty Dije aka sauke ta saboda babu halin zaman ta agidan su Ibrahim ko gidan Yusuf , Kasan cewar gidan Yusuf babu mace acikin shi Can kuma gidan su Ibrahim din yazama kamar gidan sarakkan ta ne, yan zu,, Maryam ta school ko da Ejoma ta,iso don haka dakin Maryam Anty ta kai Ejoma din, So,sai taji dadin yadda Anty Dije ta tare tankar ta taba sanin, ta ada, can,, Saboda haka bata samu wani matsala ba da take tunanen cewa za,a gwada mata kyama da farko, Da yar sallamar ta tadawo gidan cikin gajiya kamar yadda ta saba shigowa gidan,, A, zaune Ejoma take cikin shigar wata yar bakar buje daidai gwiwar kafar ta, Sai wani riga mai dan gun,tun hannu, kanta yaci kitson attachment, mai ruwa biyu, Kumbar hannun ta duk an fente shi da jakumba ja, Wani irin kallon mamaki maryam ke mata tana wani dan ja gefe guda, Kamar wace taga wani abin gudu ko kyama amms tans iya kokarin taboye, Ejoma ce ke mata sannu da dawo wa saboda ta gane maryam ranan da suka je gai,she da Yusuf da yai accident, Ejoma ta kara da cewa ya hanya, ya gajiya, sister, ? A, daddare tace, ma Ejoma yauwa, sannu ko, Dakin ta ta shiga bata zauna falon ba yadda ta saba yi idan tadawo,, Turus tayi a,dakin don ganin kayan bakuwar mai dan gun,tun buje a dakin ta, Wani wari hannci ya bugo mata dashi na man bleaching, Hancin ta ta dafe da sauri ta nufi inda taje aje room fresh din ta, ta fesa ko ina, Muryam Yusuf ne taji a falon yana magana da Ejoma cikin yare, Wani irin bakin ciki ne ya ziyarya ci zuciyar ta a lokaci guda, Anty ce ta shigo dakin don shakar kamshin room fresh din da maryam ta fesa tajiyo shi daga falo Tasan halin maryam tana iya shuka masu tsiya yanzu, Sunan maryam din takira wace ke tsaye tana mai da kwankon turen kamshin, Maryam ta amsa da na,am anty ? Anty Dije tace cikin tausa muryan ta, Don Allah maryam kada ki nuna wa wanan bakuwar wani abin kyama , Kaunar Yusuf ne anzo da itane zata musulun ta zuwa jumma, ita ma, Maryam zatai magana anty ce ta tare ta da cewa Kin san dai Yusuf ya can,canci komai a gurin mu, Saboda irin yadda yai wa iyayen mu mu,ma kin ga ko dole mu karbi nashi uzurin koba gaskiya ba, Kai maryam ta daga a hankali alamar gaskiya ne maganar anty, Sai a lokacin maryam ta tuna da irin halarcin da, Yusuf yai mata a kauyen bobi gurin mahaifiyar ta yar kauye, Wani irin ajiyar, zuciya maryam ta sauke mai kama da ta wahala, Fitar Anty Dije a dakin shine shigowar Ejoma dauke da wani ghana most go, Kaya ne irin dinki na musulunci, zalla akayi mata saboda tasamu sauki ibada, Cikin murna ta aje kayan a gaban maryam tana kokarin nunawa maryam cikin jin dadi, Sister ki diba kigani wanan kayan zan dinga sawa yanzu, zan koma kamar ku ni ma, Tafada tana yar dariya, zama tayi gefen maryam tana cewa sister na dade ina son inshiga cikin ku amma sai ban samu damar haka ba,sam, Tun ina karama wanan ijab da kuke, saw a kai yana burgeni sose, Har ma da saya nayi , ranan eh, nasha duka sosai a gidan mu, Tausay taba maryam da take fadar haka dole maryam din ta maida hankalin ta gurin sauraren Ejoma din, Ejoma tace ba karamin duka nasha ba fa har da kaini gurin wani malam Aminu yayi, Malam din wanda yashe, wai in yarda da Aminu aka zai sa iyayyena su yarda da musulun,ta ta, Aminu ya cuce ni sister sai yanzu ne nake gane mistake wanda nayi akai, Takare fadin maganar cikin tsigar kariyan zuciya da nadama, Tace Aminu har ciki yai min na aihu, da shi, infada maki daga karshe sai ya yi rejecting nawa, Shine brother Yusuf yadauke ni zuwa gurin shi, har Allah ya kawo min Ibrahim, Haweye ne suka dan biyu a idon Ejoma, wace ke kokari hade yuwun bakin ciki, Duk da warin bleaching da maryam ke ji gurin Ejoma bai hana ta kokarin dan dafa hannun ta ba tana cewa tayi hakkuri akwai Allah, Daya bayan daya suke fitar da kayan suna dibawa acikin yabawa, da irin kyau su, Marym a za ton ta Yusuf ya wuce ko amma may ? Sai ganin Yusuf tayi zaune a falo ya tasa computer shi a gaba yana aiki a ciki, Kamar ta koma baya sai ta gane cewa ya gan ta sai ,yadai nuna cewa bai ganta bane, Maryam taye fes da ita ta na saye cikin wasu siket da riga na lace, Dinkin dinkin siket din mai dan fitar da sura ne, balle rigar da shima dinkin shi, Irin fited din siket din ne ya wani dan matse ta dagwas, Sai dan kwalin da ta daura tun safe amma yanzu da yake a gida take tadan turo shi gaba, Ta daure bayan a can kasan gashin da ke daure da ribon Sai fuskanta ya fito wani dan feyau da shi kamar wata, A, class lady,,, Sai kamshin turen tana Madina da take yawan amfani da shi Da ya gauraye falon sai kamshi take yi kamar kulun, Takalman ta na gida plat shoes suke saye a kafar ta, Anty Dije tana kitchen tana tuka tuwon dare da take yin Maryam sanu da taron bakuwar ki fa, Nagode kwarai da yadda naga kin kar be ta a matsayin ta wace bata sallah kamar yadda nasan sam bakya,son hurda da irin su, A sanyaye ta ce mai ai bakon ka rahama ce, a gare ka don baka san alherin da yazo ma da ita ba, Ya lumshe ido ya sa hannun shi guda ya rufe computer ta shi a hankali, Kallon ta yake yi a cikin natsuwa na yadda ta jera mai magana a,lokaci guda, Ita ko maryam daga haka ta wuce abin ga zuwa gurin da suke aje abinci, ta bude kulan don taga ko may Anty ta dafa masu da rana, Shinkafa ce dafa duka, dai dai lokacin da anty ta shigo falon ke nan da goyon Abubakar a bayan ta, Maryam sai yanzu na tuna cewa dafa duka nayi ina Allah Allah in dan dafa maki wani abu sai kuma na shafa sat, wallahi Cikin sanyin jiki maryam ta ce yar ta ai ba komai zata jira har a gama girkin dare ta ci,, ai, Yusuf na jin su sai bai ko kalli inda suke ba yai kamar baiji abin da,sukeyi ba, Bai wani dade ba yafita lokacin duk suna ciki gaba dayan su, Sai, dawo, wan shi suka gane dauke da ledoji a hannun shi, Kayan su fruit ne da snacks sai drinks kala,kala, leda guda, A sanyaye yake cewa anty ga shi nan abawa kowa ya dauki abin da yake so, Kuma abar Assalam yadauki duk abinda ran shi ke so a ciki, Duk da anty dije tagane cewa saboda maryam ya sayo don yaji ana cewa bazata ci dafa duka ba, Mamaki tayi sosai da irin halin halarcin rayuwa irin na Yusuf , Sai tunda yafita lokacin bai kara dawowa gidan ba har zuwa dare, Anty ce tai karfin halin buga mai waya don taji ko lafiya bai zo cin abinci ba, Sai cewa Anty ya yi tayi hakkuri ba zai samu zuwa ba ya tafi wani guri Dariya take mashi a lokacin tana cewa kodai ya tafi gurin sarrakuwar ta ce, Maryam wani haushi ya kama don dai ita kawai haka taji bata kaunar Sadiya a rayuwan ta, Tafi mai kwadayin ya samu wata yarinya kaunan Safiya da ake cewa Sariya, Sariya tana da kyau ga kuma ilimin addini sosai a tare da ita, Amma wanan sadiya din inbanda fashion da nuna tsawo bata san komai ba, Muryan Ejoma ce, kecewa gaskiya sister bana son zance yariyan nan da brother sam, sam, Wai kin san may rana ya kirata a waya yace ga maman Choima su gaisa, Kawai sai cewa tayi ita wai batasan yadda zata gaida ita ba gaskiya, Amma kin san may wallahi ni nagane nufinta sarai saboda muna Christian ne fa, Kin san wasu mutane basa iya boye kyamar su a gare mu, Shiyasa nima da yace a wanan gidan zan sauka da farko har na shiga damuwa amma sai gashi daga baya yake ce min da kaina zan bashi labarin halinkirki naku, Maryam na,jin su sai tai dariya kawai don tasan ta kuru da an raina mata hankali Don dai da farko tayi niyar nuna rashin mutuncin hada ta daki guda, da Ejoma da akayi, Gurin da zata ajewa Ejoma kaya take dan gyarawa, Sim din da ta dade da boyewa, ne tagani ya fado daga inda ta boye, Cikin sauri ta,dauka ta na dubawa a hankali cikin dubara ko wani abu ya samay shi, Sawa tayi acikin wayanta don ta diba ta gani ko zai yi, Kira guda ya shiga cikin muryan shi mai kama da mai jin barci, Assalamu Alaikum, wani iri taji a zuciyar ta,da sauri ta kashe wanya takoma saman gado ta zauna, Text ta rubuta mai kamar haka, Tai,mako a cikin addini sadaka, ce ita sadaka riga kafin matsifu ce, Ka, kara taimako a saman taimakon da kakeyi ka kara ganin alheri a rayuwan ka, @@ Ya dade yana kara nanata karantawa yana mamakin mai turo mashi da wanan texts din Don yadauka tunda ya musulunta andaina ke nan ,sai gashi yau yaga mai Shine a tare da,Sadiyar shi zaune a cikkn motar shi, Suna hira don tun da yazo garin yaune karo na biyu da yazo gidan su hira, Wani kanin mahaifintane yazo zai shiga gidan nasu a lokacin Ganin bakuwar mota akofar gidan na su ne yasa shi da,katawa bai shiga ciki ba kamar yadda yai niya, shiga. Yaran yake tambaya ko motar waye a kofar gidan nasu, Wani dan yaro cikin wasu dinkin yadi blue yaje cewa baban nasu ai anty sadiya ce da saurayinta, Kamar ya wuce amma sai wata zuviya tace yahe yagani kowaye, Ganin shi tafe inda suke yasa Yusuf yai saurin fito daga cikin motar Har kasa ya tsugun na yana gaida kanin mahaifin nata dace shike bi wa mahaifin ta gurin haihuwa, Bai karba gaisuwar da Yusuf ke mashi ba sai nuna shi da yatsu yakeyi, Yace kai Sadiya ashe abinda ake fadi a kan ki gaskiya ne, Yanzu ace kin rasa wanda zaki jawo muna sai wanan Furen Jujin, Dam gaban Yusuf yafadi don jin sunar da aka kirashi dashi, wai FUREN JUJI, Mutumi yaci gaba da fadin wa zaki jawo abin kunya ke da mahaifinki, Don mutanen gari su ce kwadayi yasa muka baki Dan Ka Tuba, watau, (TUBBABE), Kuka Sadiya tafara yi wi,wi don jin kanin mahaifin nata yafara nuwa Yusuf halin shi,na jahilai , Barin fada maki gaskiya badai acikkn zurian mu ba Sadiya, Don babu mai kawo muna dan gin kafirai a gida wai jikoki, Ya juya inda yusuf yake duk kai a kasa don ji yayi kamar kasa ta tsage ya shige irin yadda yake ji, Yace wa Yusuf din tun wuri kaje ka bidi irin naka ba a gidan nan ba kaji,,, Juyawa yayi ya shige cikin gidan nasu yana ta zabga masifa shi daya, A, hankali ya juya bude mota yashiga Sadiya wace kanta yake a duke tana ta faman rusa kuka wiwi, Da kyat Yusuf yai gyaran murya ya ce ta yi hakkuri tabar wa Allah komai yafi, Ita ko sai hakkuri take ba Yusuf din cikin kuka tana mai mashi magiya cewa kanin mahaifin nata baida hankali sosai ne, A dadafe sukayi sallama da juna yatafi zuciyar shi a cushe kamar zata fito mai, Don irin cin fuskan da akai mai yai mai muni,har ji yayi kamar ba,zai iya tuki ba,,,, Tunda yadawo yake zaune a falon shi ji yayi tankar kan shi zai tsage mai a lokacin saboda irin ciwon da yakeyi mai, Ga zuciyar shi na mai wani irin soya kamar zata fashe mai, Zaune yake asaman kushin ya mai da kan shi baya saidai kuma yadafe goshin shi da hannun shi guda, Wasu hawaye madu dumi yaji sun gangaro mai a fusaka saboda tuna sunan da aka kira shi dashi, wai FUREN KAN JUJI, Ya Allah ya furta a hankali yace Allah kai kasan dalilin yina a haka, Nakuma gode maka ya uba giji na da ka bani ikon bin hanya madaidaiciya,, Idon shi ya kara lumshewa yana ma zubbda hawayen bakin ciki, May ye laifin shi a yanzu kuma bayan dashi da su duk matsayin su guda a gurin ubangiji, Da wanda yai she kara dari da wanda ya shigo yau duk abu guda suke a gurin Allah subbahanahu, wata,ala, Dangin shi kuma ko ya suke shi ba zai guje su ba saboda sune nashi, Bai san ko daga cikin su akwai mai rabon shiga musulunci ba a ta dalilin shi, Irin tunanen da yai tayi ke nan har dare ya raba tsakiya ya kasa barci, ga wani daci da yake ji a makoshin shi, Sai zafi da yaji jikin shi ya fara yi kamar wanda fever ke shin kamawa, Kiran wayan shi take tayi tun tana jin yana,shiga sai ya katse layin da kan shi, Anjima kadan kuma takara kiran shi amma sai taji ya katse, wayan Daga karshe ma sai taji kawai ya kashe wayan ma gaba daya, Tsuki tayi ta wurgata da wayan ta kwanta taci gaba da zubar da hawayen bacin rai, Tana mai Allah waddai da irin halin baba Ado wanda bai san darajan addini ba sai kuri da shi, Ko a wani nafsi akace mai an kya maci auren wanda ya tuba Ita dai a sanin ta baba Ado ya hada da al,adace kawai in bashi ba don mai zai kira Yusuf din da wai furen kan juji,, Sai zuwa dare tayi taji kira ya shigo mata a waya lokacin har ta yi shirin barci, duk da tasan cewa yau ba zancen barci gare ta, Jibrin tagani barobaro a wayanta, saida tai tsuki tadauka da fadin cewa kaga damar daukar wayan Don kaga ina kiran ka shine harda kashe min layi ko, Dariya yayi mata ya ce haka kawai zan yarda ki damay ni ga banza Kuka ta farayi tana aheda mai abinda Baba Ado yaiwa Yusuf yau da yazo gurin ta, Innalillahi kawai Jibrin ke ta nanatawa alokacin saboda maganar tazo mashi a ba,zata, Yace wai ko dai da gaske Baba Ado bai da hankali kamar yadda mutane kece mai mahaukaci Ra,ra,shin ta ya yi yace ta bari yaje gurin yusuf din yagani ko ya akayi, Yusuf wanda alokacin yana can cikin bargo yana jin wani irin amai da zafi na damun shi, Kuma duk yabi layin wayan shi ya kashe gabaya ba mai kiran shi ya samay shi a lokacin, Jibrin gidan Yusuf din yazo direct don yadiba shi am.a sai yaga duk ko ina a kulle yake, Dole yakoma badon yaso ba don yana gudun ya ta dashi daga barci, ZEEE. MAKAWA [3/24, 2:21 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN, JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, Ya Allah mun gode ma dakayi acikin Al,uman Annabi Mohammad S,A,W, Allah kaba ikon koyi da Sunnan a tafarki mai umfani, Ya Allah katai make muslimi kasar Syria da ma na duniya baki daya, Ameen Ya Allah👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Har muslim sha dayan rana ba labarin Yusuf anty dije sai fada takeyi cewa ya na biwa ta mutane yaki zuwa ya yi breakfast, Ganin sha biyun rana yana batun yi yasa takara, kiran nobar wayar shi ko zai shiga, Cikin sa,a tasamu kira guda ya shiga, sai dai wayar tana ta ruri har ta kusa katse wa ya samu da kyat yadan daga wayan, Yanayin muryan shi kawai ya wadatar da mutun yasan cewa yana acikin wani yanayi Gaban Anty Dije ya fadi Dammm, Jin muryan kanin nata a cikin wani bakon yanayi da bata sani ba, Cikin rawar murya tace Yusuf baka da lafiya ne ko may ke faruwa haka, ? Dan ajiyar zuciya ya sauke mai dan karfi a lokaci guda, Hankalin Anty duk yatashi ga network kuma ba kyau bata jin shi sosai abinda yake cewa, Cikin daga murya take kwalawa maryam da ke kitchen kira, Da sauri maryam ta iso falon don dajin kiran tasan cewa kiran na sauri ne, Hannunta take kokari gogewa a lokacin saboda ruwan dake a hannun nata,, Anty ce ke kokarin mikewa tsaye tana sabe da Abubakar dake shan nono, Maryam don Allah shirya ki je gidan Yusuf ki dibo min ko lafiya, Don kin ga ba dama in aiki wanan Yarinyar don kada yan uwan ta su ganta a agari, Wani irin abu maryam taji amma ba tada yadda zatayi don ba zata iya yiwa antyn ta musu ba, Jiki ba karfi ta shiga dakin ta tafara shiri, wasu, dongon rigar material ta sa inda tasa wandon lages ta ciki, Sai kamshin da ta feshe jikin ta dashi tsab kamar ba a kitchen ta fito ba duk da dama tayi wankan safe ko, Ita aganin ta ba kwalliya tayi ba amma duk wanda ya gan ta zai zata gurin wani buki zata alokacin, Kudin mashin anty ta mika mata, har zata fita takara kiran ta tace da ta tafi mai da kayan breakfast din shi can, Dole haka maryam ta dauki kayan niki, niki zuwa inda zata tari mai mashin, Kofar gidan kamar a rufe take amma dai don ta tabbatar sai ta dan tura a hankali, Mama ki tayi lokacin da taje a bude yake, A,she tun da yatafi, massalaci sallah a,suba da yadawo bai kara rufewa ba, A,hankali take tafiya, ta ratsa wani dan dogon corridor sanu a hankali ta isa kofar shiga folon ciki, A kwance ta hango a falon cikin gidan a kasa, bisa carpet, Yana sanye da da wata yar far singlet da wando short, nica, Kamar ta koma amma kuma yadda taga yanayin kwanciyar shi, yasa ta kasa wuce wa, Hannun shi guda yana dafe da goshin shi, A hankali ta isa gurin shi, ta durkusa daidai tsawon shin, Gaban tane ya fadi ras don ganin yadda ya koma cikin kwana guda, Ta kasa wani magana a lokacin sai kallon shi takeyi kamar taga wani abu, Kamshin maryam din yaji a lokacin hakan yasa shi saurin bude idon shi, Tabbas maryam din ce a gaban shi ba wai shake bane, Cikin wata irin murya yai magana tankar ba shi ba, Yace Maryam, Kece a tafe yanzu ? A sanyaye tace mai eh nice Anty ce tace inzo in diba ka ko lafiya ? tun, jiya baka zo cin abincin ka ba, A cikin zuciyar shi yace Allah sarki Anty na, Sai,da ya lumshe idon shi sanan ya ce mata, wallahi maryam, Bana jin dadin jikina ne tun jiyan kirji na kamar zai fashe , Wani irin tausayin shi maryam din taji, don yadda taga ya dafe kirjin da zai dan tashi zaune, Ya,dan daga kan shi ya kalle ta, yace na so inyi karfin halin zuwa gidan amma ba,zan iya ba gaskiya, Wani iri taji a ranta sai ta dan lumshe idon ta a lokacin taji hannun shi cikin nata, Wani irin zafi taji radau alamar yana cikin zazabi mai karfi a tare dashi, Zuwa kirjin shi yakai hannun nata yana cewa maryam kirji zai fashe saboda yadda nake jin shi, A hankali maryam din ta saurin cire hannun ta a cikin nashi, Shikuma ya maida kan shi saman carpet din ya kara kwantawa, Murywn ta yaji tana cewa tun yaushe ne baka da lafiya ya Yusuf ? Yadan kalle ta a sanyaye idon shi sunyi wani lusu,lusu da kyat yake iya budewa, Tun jiya nai bayan nadawo gida, nafara jin haka, Tace to ka kasha magani ne, ? Kai ya girgiza mata tankar yaro karami, Mikewa tayi tsaye daga inda take a tsugune tace barun hada ma ruwan wanka tukun, sai kaji dadin yin break din, Tamike a hankali ta nufi cikin kuryan dakin ta hada mai ruwan wanka, Har da maclen sai da maryam ta matsa mai a brush tare da aje mai tawul a gefe, Sanan tafi tace mai bissimila Da kyat taga ya mike tare da taimakon dafa kujera da bango, Maryam na ganin ya shige ciki tai sauri cire hijab din ta, Ta fara gyara mashi falon duk da tsab yake baida wani datti so sai, Saidai kuryan dakin ne keda dan gyara shima kafin yan mintina yakoma tsab, Ta kwashe kayan wankin da taga a wa,wa tse takai, bakin kofar bathroom din ta aje, Yan,kudaden da tagani ta mayar a karkashin filo ta aje, Traveling baga din shi ta bude tafitar mak da wasu simple kaya marasa nauyi, ta aje agefen gado, Ta koma falo ta aje mai kayan break din ta yadda zai iya jin saukin ci, A kofar dakin ta tsaya tana mai ce mai Ya Yusuf ga abin karin nan fa kada yai sanyi, Yana zaune a bakin gado lokacin daure da wani farin towel iya gwiwar shi, Ta juya zuwa falon batare da tashiga cikin dakin ba ko daga labulen kofan, Tun a cikkn dakin Yusuf yaga canji don yaga ko ina fes tankar ba wanda ya,ba ri da kazanta ba kafin ya shiga wanka, Haka ma falon yake tass kamar bashi ba sai kamshi ke tashi hade dana cooler Gefe tadan koma nisa dashi kadan tana kallon yadda yazauna ya harde kafa guri guda Amma yana cusa abinci da kyat kamar mai cin magani, Kiran wayar Anty ce ta shigo a wayar maryam din Cikkin daga murya Anty ke cewa maryam ya akayi gaki shiru baki dawo ba balle muji ko lafiya, Ganin zuwa kawai tace wa Anty n nasu batarr da tai mata wani bayani ba akai, Ganin maryam na kokarin hada kayan da yaci abinci yasa shi sauke nunfashi har sai da ta juyo, A hankali ya furta mata nagode kwarai maryam, ina gaid Anty, Jibrin ne yashigo falon da sallamar shi yana cewa Man don Allah dai kayi hakkuri wallahi naso zuwa tunda safe Sai kawai muka tafi unguwa ni da baba diban wani dan uwar shi da bsi da lafiya, Ashe haka kukayi da wanan mahaukacin Ado wanda bai san Allah, ba, Shi har ya,na da ikon da zai gayama wanan magana haka, Ai gara kai sau miliyon a,kanshi, wanda ko addini bai sani da har zai kiraka da wai tubabbe dan furen juji, Kai kawai Yusuf yakada yana murmushin karfin hali, Sai kuma ya tuna da maryam wace a lokacin har ta gama sa kayan acikin basket ta mike tsaye ko, Ganin Yusuf ya kalli maryam yasa jibrin shima saurin kallon inda maryam din take, Sai alokacin ya tuna cewa tana gurin ai, bi kamata yaita sake layi ba haka, Koma maye ai ta gama ji ko a lokacin don haka tai masu sai anjima ta wuce zuwa ciki abinta Zuciyar ta fam da magana takama hanya, sai muryan Jibrin taji a bayan ta yana cewa tazo ya sauke gida, Kai ta girgiza acikin murmushin karfin hali tana cewa a,a ka koma gurin ya Yusuf don kada a barshi shi kadai, Ba musu jibrin ya koma amma Yusuf din yanuna mai cewadan Allah yaje ya kaita kawai ai yaji sauki, ko, Jibrin yana fitowa ya hango har maryam ta hau mashin sunyi nisa da tafiya ko, Tsab maryam ta labartawa Anty abin da ya samu Yusuf, Sai,dai ta boye wa antyn zancen da taji shi da jibrin su na yi, Saboda ganin Ejoma a guri duk da dai dama bawai fada zatayi ba, Da su Anty zasu koma sam Maryam taki yarda ta kara bin su, Don haka ita kadai ce a ka bari a gida lokacin don duk yaran su bi su, Wanka tayi tai sallah la,asar tare da fara gyara masu gida, Don daga Anty har maryam basu kaunar ka,zanta sam a rayuwar su, Shiyasa koda yaushe zaka samu gidan tsab a cikin gyara ga kamshin turaren wuta yana tashi, Abinci tai masu lafiyayye tuwon farar shinkafa da miyar taushe, yaji busashen kifi, Har tagama ta sawa kowa a cooler su Anty basu dawo ba sai zuwa yamma suka shigo agajiye, Take cewa maryam ai Jibrin ne yawuce abinshi bai dawo daukar su ba,, Taji dadin girki da tasmu maryam ta idar don hakane duk inda zata in har maryam na gida bata shakar komai a fanin girki da sauran harkan kula da gida, Sai zuwa dare Yusuf yasamu yadan lalaba yashigo garin don ya mike kafar shi,, Direct gidan Anty dije ya fara zuwa duk da yaso yatafi gidan Abdulsamad akan zancen musuluntar da Ejoma, Wasu yadine farare masu laushi a jikin don har zaka iya gani yar far singlet din da yasa ta ciki, Duk da yaramay sai dai har yanzu hasken shi yana nan bai dushe ba, Yanayin shi kawai zaka kalla kasan cewa bai jin kwarin jikin shi still, Maryam ce aka umurta da tayi serven din shi a lokacin, Duk da a rayuwan ta bataso ba don har tana shirin kwanciya a lokacin, A sanyaye take yin komai yana zaune tare da Assalam suna hira, Cikin murya irin ta, marasa lafiya yace maryam, Juyawa tayi a hankali tana kallon su, sai yanzu taga irin yadda ya kara zabgewa da kyau, Yace may yasa dazun nace kada ki hau mashin kika hau, Maryam i hate inga mace a saman mashin wallahi, Baki taturo gaba irin nuna ina ruwan ka to da ni da har zaka samin ido, Batare da ta kalle shi ba ta ce mota gareni da zan daina hawan mashin, Ai nima nasan mutunci na kuma har kullun ina kokarin kare kai na, Cikin sake wani malakacin murmushi yace, Mota kike so maryam ? Sai da takalle shi da kyau tace, Ai don ina yar talakwa ba zan debe rai ga rabo ba ko Waya san gobe banda Allah, Kan shi yadafe kamar wanda ya ji ciwo yace, Ho, ho ho ho maryam wa ya fada maki nufina ke nan, Da talalka da mai arziki ba duk Allah ne yayi su ba ? Allah yana ba wa wanda yaso ba don wani dalili ba , Yana kuma hanawa wanda yaso ba don wani ya kishi ba, Sai da ta kau da kai gefe tace, A wurin wasu ke nan, da sauri ya ce subbahanallah, Ido ya zuba mata yana mai langabar da kan shi kamar maraya, Ya ce nidai don Allah alfarma nake nema a gurin ki sam bana son,,,,,,,, Karasowan Anty Dije ya hana shi karasa zancen nashi, Zama tayi a can saman dayan kujerar lokacin da maryam ke kokarin tarfa mai man shanu a cikin miyan da ta zuba mai, Wayar shi tai kara maryam tai sauri daga kai ta dube shi, daga inda take, Cikin harshen IBO yake magana Abdulsamad ne ke tambayar ko zai samu shigowa Yadan bashi ansa a ta kaice kawai, Sai kuma yai shiru yana sauraren shi sai daga bisani ya amsa da to cikin hausa, Kashe wayan yayi a lokacin maryam na kokarin, barin gurin yace mata atashi lafiya, Maryam na shiga daki ta samu Ejoma tana kokarin gyara masu gurin kwanciya, Ce mata tayi ta kwanta kawai ita zata hau kushin kamar jiya, Kwana biyu tsakani ranan jumma,a aka musuluntar da Ejoma,a cikin massalacin jumma, ta garin kwantagora, Sosai Anty tai ta aikawa mutane da abin sadakar da sukayi don musuluntar nata, Kafin marance yayi saiga kungiyar Iyamurai sunyo tsinke zuwa gidan Abdulsamad wai zasu kona, Su kuma matasan gari sukace wallahi suna sa ma gidan wuta sai sun kashe ko wani IBO dake a garin kuma su kona su, Saida aka kai su gidan masu gari suka ja masu kunne so sai, Duk basuga laifin Yusuf ba saboda shi yana da kudi, kuma mahaifin shi nada su, Abdulsamad bawan Allah suka lekewa kawai, kamar zasu cinye shi danye Amma shi ko a jikin shi don kawai Allah ya tsawa ba wai wani ba, Maryam ce ta shirya Ejoma wace yanzu ta koma Na,imat, Dinkin riga da zani da hijab tasa tare da yin kitso irin na hannin na hausawa, musulmai, Sosai suka koya mata yadda zatai wanka da sauran abubuwa, Sai faman washe baki take yi tankar wace akaiwa bushara, Itama maryam din a cikin wasu koren atamfa super wax take, an masu dinki na half gown, da wani shara sharan gyale da bai hana ganin dinkin nata a fili, Sai set din wasu dan kunnen na fashion masu kyau da daukan ido, Ganin bazasu samu shigowa yau ba saboda zirga,zirgan da sukeyi yasa anty cewa takai masu abincin su, Idan akwai abin da maryam tai hating to wanan aiken don ita aganin ta ai su yakamata suzo su dauka tunda suna da abin hawa, ai Amma ta ya za,a dinga turata kai ma kato wanda baida mata abinci haka, Kamar tasan tunanen da maryam keyi sai kawai taji tace mata kutafi da Assalam ko, Tun daga wajen gidan zaka gane cewa bashi kadai bane a gidan, Saboda abin hawan dake wajen gidan fiye da guda, Da sallamar ta tashigo gidan dauke da kulolin abinci masu girma, Idon su kyam a kan ta har sai da ta dan ji kunyan kallon da suke mata, Kan ta duke a kunyace ganin yadda suke kallon ta, ta wayance Yusuf ne yace ke ce tafe da ranan nan maryam karaso mana, Direct gurin da dining table din tanufa don ta aje kulolin, Ko may kuma ta tuna sai taja burki ta tsaya wanda hakan yasa shi yin ajiyar zuciya, Daidai gurin gefen kujerun ta aje kulolin kawai sai ta mike, Maida kallon ta tayi a kan su tace cikin taushin iji Anty wai akawo maku anan, KB ne yace tab ai mukn yau sadiya ta cika muna ciki fam da kayan zaki, Da gagawa Maryam ta mayar da duban ta ga Yusuf, Wani sanyi maryam taji gwiwar ta yayi da kyat ta dan mike gami da kakaro wani murmushi tace , Au ashe ma kun ci abinci Anty ko tana can duk ta damu, A sake yace mun ci ko sunci ki zuba min pls don ni yanzu nake da niyar zuwa inci a can, Kamar da gayya Maryam ta cika mai plate dam da abinci da yaji naman rago, Sai da yadan daga kanshi ya kalle ta ya kalli abincin sai kuma ya mika hannun shi yakarba, Gurin karba yai kamar hankalin shi na gurin Assalam sai ya hada da hannun ta ya rike, Cikin sauri maryam taja baya da abincin ya bare mai a jikin shi, Batai wani dadewa ba tacewa Assalam su tafi amma sai Yusuf ya ce mata Su jira shi har ya kare cin abinci sai ya sauke su gida da kan shi, Zamu iya zuwa ai mai mashin na waje yana jiran mu tace mai, Abincin dake a gaban shi ya ture gefe ya ce mutafi na sauke ku kawai, Wani kallo maryam tai mai ta tsura mai idanu sai kuma ta mike ta fadin Assalam mutafi, Tariga kowa fita don shi ya tsaya daukar key sai muryan Jibrin yaji yana cewa Something is fishing somewhere,, Kamar ya tsaya yai mai magana cewa bai son haka kada yarinyar ta raina shi, Sai kuma dai ya sa kai kawai ya wuce don idan ya tsaya zasu iya hawan mashi, Shi ko sam baya son haka, don bai so ace gurin zuwa gidan shi wani abu ya samu yar mutane, Duk da yasan cewa biyayya ne kawai ke sa tana daurewa tana mai abu saboda Antyn ta, A kofar gidan ya samay su tsaye suna jiran shi sai dai fuskanta a cikin damuwa yake, Gaba take zaune a tare da shi Assalam yana baya zaune yana ta wasan shi, Murya kasa,kasa yace, may yasa baki fadawa Anty zancen da kikaji muna yi da Jibrin, ba ranan, ? Saida tadan juyo ta dube shi sai kuma ta juya gurin window motar ta mai da hankalin ta , Kamar bazata bashi amsa ba sai can tace, saboda maganar bai shafe ni ba, Kuma ban san ko may ke faruwa ba sai kawai in sa kaina aciki, Wani irin hucin iska mai zafi ya furzar da ga bakin shi, Yadan daki sitiyarin mota da hannun shi sai kuma ya numfasa, Daga haka bai kara cewa komai ba har zuwa lokacin da suka tsaida motar su kofar gidan,,,,, ZEEE MAKAWA [3/24, 2:22 PM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA Allah ya karawa Annabi daraja, Ya Allah ka daukaka musulunci Ya Allah ka sa mudace da Rahaman ka, 👏👏👏👏👏👏👏 Duk yadda mutum ke tsan mani hankalin yan church ys tashi sosai, Hakan yasa suka mai da hankali sosai wurin jawu hankalin mutanen su da cusa masu ra,ayi Daga can gurin shugaban nin su sai suke ganin cewa ai wani sakacine da dama mutanen suka bayar, Shugaban Catholic churches gaba daya na kasa ne da kan shi ya sauka garin na kwantagora, Sai da ya je gurin maimartaba ya kai gaisuwa Inda ka basu dokoki kamar yadda ake wa kowani irin shigaba na addini don gudun tayar da tanzo ma ko wani tashin hankali, Bayan sun koma church ne suka zaune yin mintun din su na shuga ban nin su, Idan zakaji irin kudin da suka ajewa jama,an kasar ta kwantagora da kewayen ta sai mutun yai mamaki sosai, Badon komai ba sai don kawai su ja ra,ayin masu raunin ima zuwa gare su, Da kuma wa yan da ake ganin cewa sun karkata ne kila don talauci, zuwa cikin musulunci, Sunyi rabon mashi,mashin da ke kuna hawa da na dinki ga mutanen kawai Inda hankalin mutane sosai ya irin wa yanda basu da addini suka dinga shiga kungiyar su, Father da kan shi ya shirya yadda za,a tunkari Yusuf, da Abdulsamad, Yana zaune a cikin office din shi yana breakfast, Cup ne mai dauke da ruwan shayi masu zafi yake korawa a hankali, Don shi al,adar shi ce,shan tea mai zafi har ya dan kona baki, Amma shi agare shi saboda sabo da zama kasar America yasa bai jin zafin Dan tiririn ruwan na tashi saman cup din yana yi sama, Yayin da sanyin AC ya gauraye office din duk safiya ce yanzu rana bawai wani yi, Sakatariyar office din shi ce ta shigo da sallamar ta , Kallon ta yayi da cup din tea din shi a hannu ya ce, yadai Helen,? Cikin dan rusun nawa tace boss kayi baki fa , Haka kawai yaji gaban shi ya ba da damm, to wasu baki yanzu zasu zo mai a wanan lokacin kuma baida appointment da su, Sai kuma zuciyar shi ta nasa mai cewa kila wasu masu bukatar wani abune, Yace wa Helena tace su shigo, Helen tace da har na ce su koma kawai tunda basu da appointment da kai, Don na lura ba harkan business bane ya kawo su don sun min kama da masu preaching, Wani tsawa yadaka mata ya katse mata dogon zancen da take ja dashi, Ya ce ki ce su shigo nace maki Umurni na baki ba wai uzuri ba pls, ki kawo min ba , bayan kin fada masu cewa ina ciki ko, Don su ga na yi masu wulakanci na hana su gane ni ko,? A yadda Yusuf yai maganar cikkn tsaw yasa Helena, jin tsoro, da sauri ta fita zuwa yiwa bakin iso, Ba ai wani bata lokaci ba sai gata da bakin sun shigo a tare tana masu iso, Yana kokari a je cup din tea din shi a lokacin suka hada ido da Peter wani class mate din shi tun primary a kwantagora, Yanzu Peter yana aikin banki ne a Enugu, amma dai iyayen shi suna zaune still a nan northern Nigeria, Sai kuma wasu mutun biyu da yake ganin kamar ya san su a da can, Yai masu sannu da zuwa duk da bai san abin da ya kawo su gurin shi ba, Yace wa Helena ta kawo masu abin sha, inda ya nuna masu gurin zama, Bayan sun zauna sai gaisawa ya biyo baya inda suke ta yiwa juna ya bayan rabo, Ganin yadda Yusuf ya koma kawai yasa suka ga yai masu wani irin kwarjini a fuska, Saidai ya lura da cewa daga cikin su ba wanda ya sha drinks din da aka aje masu a gaban su, Sai da suka natsu Yusuf ya juyo yana fuskantar in a serious face ya ce lafiya dai, ko nagan haka,? kafin su yi magana sai wani daga cikin su ya fara jero addu,oi kamar yadda sukeyi a koda yaushe, Ameen din da suke fada shima shi yake fada tunda duk addua ce ai, Ganin yana karba masu yasa suka dan samu karfin gwiwa, kokarin fuskantar shi, Saida suka gama wanda yafi shekaru a cikin su ne yafara magana da cewa, YUSUF munzo ne don mu fuskanci juna da kai akan juyawa Jesus crisis baya dakayi, Munzo ne on behalf of our members,na Catholic churches, don mu baka hakkuri akan duk wani abin da mukai maka har ka canza, religion din ka, Yusuf ya girgiza kan shi yana cewa ni ba kumin komai ba kawai don na gano cewa Islam itace hanya madaidaiciya, Kunga yanzu dai nakai munzalin da idan ina ra,ayin abu zanyi don kai na kawai, Ido suka tsura mashi gaba dayan su suna sauraren shi, Yaci gaba da cewa ban shiga cikin Islam ba sai da na tabbatar da na samu kwakawaran hujan da zan kafa wanda har yajani zuwa, cikin ta Ni ban shiga don wani ko wata ko kuma don kwadan wani abu ba, kawai don ra,ayin kaina nashiga, Mikewa wanda Yusuf yakira da Peter, yayi har zuwa gaban Yusuf din yadan dafa tebur din suna fuskantar juna, inda yace mai Look Joe, daga million daya har zuwa goma zamu iya baka don kawai kadawo ma addinkn ka daka bari,, Cikin wani murya mai kama da tsawa Yusuf yace mai , Na fada ma cewa badon wani abu nashiga wanan addinin nawa ba kawai sai don irin hujjojin da nake dasu akai, Mikewa yayi zuwa wajen wani serve dake a cikin office din inda yasa wasu nombobi gurin ya bude, Kudi ne sabbi kar ya kwaso yakawo masu gaban su wanda kallon su kawai zai sa mutun yasan cewa sunkai miliyoyi, Yace bani bukatar kudin ko kowani abu kawai don tsira da rayuwata nashiga wanan addinin Yakare zancen yana mai tura masu kudin a gaban su lokaci guda, Wanan ya kalli wanan wancan ya kalli wancan, Jiki ba kwari suka mike tsaye saboda sun san cewa sam ba riba akai, Har sunkai kusan kofa Yusuf yakira sunan Peter yana mai ce mai i,hope for daga haka kun rabu dani kenan pls, Ya hada hannayen shi guri daya alamar yana rokon su da sufita harkan shi pls, Ba wanda ya kara ko juyowa suka sa kai zuwa hanyar fita, Zuka tan su cushe da bakin ciki saboda sun san cewa sun rasa Joe din ke nan har abada daga cikin su, Gashi kuma yayi nisa ta yadda basu iya jan ra,ayin shi ba sam, Wani irin tsaki ya ja yace batatu kawai, Sai bayan fitar su ne yadaga hannu yanawa Allah godiya da irin baiwar da yai mai ga ta addini ga kuma dukiya, Sonny ne yafado mai arai inda yaiwa Sonny din adduan shima Allah ya sa ya gane gaskiya, Ashe har da Abdulsamad sun ziyarta inda yai masu kaca kaca da cewa kada su kara tuna shi daga cikin su, Sai dai Ejoma ce basu san inda take ba har yanzu tukun,,, Tun bayan tafiyar Yusuf maganar ta tsayawa maryam arai so sai, Sai dai kuma ta rasa hanyar da zata fadawa antyn ta cewa ga halin da ake ciki a zancen, Da bara ce ta fado mata na ta ba wa Anty shawaran zuwa dubo Sadiya din, Suna zaune a tsakar gida tana,wasa da Abubakar din Anty, Sai ga kiran yusuf ya ahigo a wayar Anty Dije sun kai wani lokaci dashi su na dan hira, Inda yake sheda mata cewa ya je gurin ya Iliya mijin Anty yace zai shigo kafin Azumi, Tai mamakin jin cewa ya tafi gurin shi nan yake sheda mata cewa akwai wasu kayan su da za,a shigo da su sune yaje yin clearing, Nan yake tambayar lafiyan su Assalam da sauran su amma dai bai tambayi maryam ba, Itama dai anty sam bata dauki wanan a bakin komai ba , Sai zuwa dan lokaci da kare wayan na su ne maryam take cewa Antyn ta Gaskiya Anty yakamata mu tafi gidan Sadiya mu diba ta kada tace ba ki taba zuwa, Haka dai tai ta cusawa Anty Dije ra,ayi har dai daga karshe ta amince da cewa zasu, tafi su uku da yara, Bayan kwana biyu da zancen shiri sosai sukayi i dan ka gansu zaka zata wani guri can zasu, Ashe wai duk shirin zuwa duban budurwan Yusuf ce, Kai su akayi a,cikin wata motar da maigidan Anty ya saya ya barta a gida, Sadiya tana zaune tare da wasu kan,nenta suka kallon tv a dakin mahaifiyar, su, Suka ji sallaman mutane, kallon su suke yi a cikin rashin sani, Sadiya din ce tagane su ta ganin Assalam a cikin su, Nan aka shiga gaisawa a tsakani inda Sadiya din ke nuna yar jin kunya, a tsakani, Mahaifiyar ta tasa aka kawo masu kunun zaki mai sanyi yaji kayan kamshi sai tashi yakeyi a ciki, Maryam sai kallon gidan takeyi irin kallon kwam din nan, Bayan fitar mahaifiyar sadiya da kannen ta ne, suka dan kara gaisawa da Anty Inda Anty kewa Sadiya kewar Yusuf, din ? Jin maganar Sadiya tayi kamar don zolaya suka zo mata, Amma kuma, sai ta tuna da yadda Yusuf ke fada mata halaiyar Anty dakuma irin yadda take son alakar su, Dago kai tayi tanawa Abubakar dake hannunta wasa, Sai kuma ta sauke kan ta cikin kwantar da murya tace Anty Yusuf bai fada maki yana fushi dani bane aiko da ya wuce bamuyi sallama da shi ba, Kuma nai ta kiran wayan shi bai daga wa, Nan da nan an nurin fuskan Anty Dije ya sauya lokaci guda, Cikin damuwa anty ke tambayar sadiya abin da ke faruwa, Bata boye mata komai ba na yadda kanin mahaifin ta yaiwa Yusuf din daren da yazo zance gurin ta, Na,imat ba tasan lokacin da tasa kuka ba alokacin, Tana cewa abin da mutanen su ke yawan fadi ke nan cewa koda Christian ya musulunta gori da hattara da musulumai zasu dinga mai har sai yafi na lokacin da bai shiga cikkn su ba, zàfi da ciwo, Nan kuma hankalin su yakara tashi ganin yadda Na,imat ke fidda hawaye, Abu ya taru lokaci guda yai wa Anty Dije yawa, tarasa da,wani zataji, Sai,da suka samu Naimat (Ejoma) tai shiru san nan suka fara magana, Maryam na zaune a gefe tai shiru tun da akafara zancen ta na mai jin zafin irin kalamin da aka ta jefawa Yusuf din, Sadiya ki yi hakkuri zan kirashi in ji may ke faruwa ne ai bai kamata yai saurin fushi ba haka, Mahaifiyar ta wace itace yar uwan Jibrin din tashigo dakin Inda take kara fada masu halin kanin mahaifin nasu dan cin mutunci, Tun a hanya Anty Dije ke ta zabga wa maryam godiya don badon ita da takawo shawaran zuwa diban Sadiyar ba da ba zasu san abin da ke nan ba,, Cikin ikon Allah ranan Yusuf bai kira anty ba sam tankar yasan da zancen, Ita ko Na,imat duk hankalin ta ya tashi saboda ji takeyi kawai ta zauna a cikkn yan uwan ta zaifi mata Kada sai sunyi aure da Ibrahim irin wanan gorin ya biyo baya, Ji tayi an dafa mata kafada A hankali ta juya don ganin kowaye maryam ce ke mata murmushi, A hankali maryam ta zagayo in da Na,imat din take zaune, Saman hannun kushin din ta zauna a hankali maryam tace Na imat kada ki sa komai a rayuwan ki pls saboda dama kin san sai an samu irin wanan challenges din, Saboda wasu basu da tauhidi atare da su just dai suna ansa sunan su musulmai ne kawai, Ki sani cewa Ibrahim dai kabilar ku guda dashi kin ga ke nan wanan irin challenges din zai zo maki da sauki, Unlike na ya Yusuf wanda in dai ba haushe mutun ne koda ace shi ya Yusuf din a cikjn musulunci aka haife shi, Zaman shi na dan kabilar ibo ko bayerabe sai sunyi suka akai, Kai koma da ace yaren da ke anan cikin arewa ne tare da mu, Kawai ke dai imani azuciya take ba,a baki ba, Don haka duk wani tunane ki daina kawai ki sa Allah a gaba kin ji sister, Kai Naimat ta daga alamar gamsuwa da zancen maryam din duk da tagirmay ma maryam din sosai amma dai yarinyar na bala,in bata shawa saboda irin halaiyar ta, Ga kuma irin yadda ita da yar ta suke kokarin koya mata addini akoda yaushe acikin sauki, Sai washe gari ya kira Anty Dije tun daga maganar ta yagane cew akwai matsala don ba haka take mai ba idan suna waya, Antyna lafiya kuke kuwa naji muryan ki wani iri kamar ba dadi yau azuciyar ki Anty Dije ce ta katse shi da cewa Yusuf may ke faruwa a tsakanin ka da Sadiya ne ? Shiru yayi na dan wani lokaci sai kuma can yace tazo gurin ki ne, Anty Dije bata boye mai komai ba tafada mai yadda maryam taga cewa ya kamata suje su kai mata ziyara, Nandai ta bashi duk wani bayanin da yadace tai mai alokacin, Tsawon wani dan lokaci bai yi magana ba sai zuwa can yace, Ànty Dije gaskiya bazan boye maki ba bazan iya auren Sadiya ba kuma yanzu, Saboda ko munyi aure za,a samu matsala sosai, daga yan uwan ta, Katse shi tayi da cewa kai Yusuf yan uwanta zaka aura kodai ita, ? , Murmushi yayi kawai yace bazaki gane bane anty kawai abar wanan zancen zai fi, Yusuf ko da sunyi challenge din ka ne ai ba yarinyar bace tayi ko ? Zan dai kira ki anty yanzu zan tafi sallah lokaci yayi, pls,,, Saida ya idar da sallah shi sanan ya kira layin maryam Maryam wace a lokacin tana daki zaune ta idar da salla itama saboda time akwai dan tazara tsakanin yadda ake sallah a kwantagira da Abuja, Cikin mamakin ganin layin Yusuf na kiran ta, ta mika hannu akai ta dau ko wayan, Da muryan nan nata zakwaikwai ta,ansa sallamar tashi, Gaisuwa ta fara yi mai tana mai kara wayar a,kunnen ta, Sunan ta yakira cikin wani irin muryan nan cikin golden voice, Maryam ta amsa da na,am Yace may ye hikimar ki na kai anty gidan su sadiya pls ? Shiru tayi kamar bazata ce mai komai ba, Wani irin nauyi da kunya ne ya lullubeta don may anty zata bari yasan cewa itace ta bada shawaran a,tafi gidan su sadiya, Karo na biyu ya kara kiran sunan ta cikin wani soft voice da yafi na farko taushi, Yace kina ji na pls karki boye min komai akai, ki fada min dan Allah,? Sani sanyi taji don ya hada ta da Allah akai, Nan take ce mai ya Yusuf a gaskiya dai ka san cewa mutumin bai kyauta maka ba ko , Bai kamata ace yai maka wanan cin fuskan ba gaskiya, Zataci gaba sai ya tare da cewa cikin yar murmushi maryam ai ba karya ya fadi ba ko,? Tunda dai ni din duk yan uwana kafirai ne ni kadaine Allah ya cire a cikin su, Kinga ii dole ne in ta samun wanan challenges din ko, ? Ta gumi tayi da hannayen ta bibiyu tana sauraren shi cikin tausayi Tana ji tankar ace itace a kusa dashi a lokacin a matsayin ta nadan uwan ta, Amma afili sai tace to ya yusuf dan Allah kayi hakuri bazan sake ba Abin ne yaci min rai sosai wallahi shi yasa nakai anty taji da kan ta don a dauki mataki akai, Murmushi yayi yace aa maryam wani mataki kuma kawai na bar masu diyar su kawai, Cikin sauri tace subbahanallah dan Allah ya Yusuf kadakayi haka pls, Saboda may maryam kinfi son ta dani yayan ki ke nan,,? Ya yariny ce wallahi akwai tausayi idan ka ganta Nan dai yaci gaba da bata musalai akai har ta dan gam su sukayi sallama,,,,,, ZEEE. MAKAWA, [3/24, 10:09 PM] Zainab Makawa: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 5⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, Wanan shafin nasadaukar ga Shahararen Admin of Admins na,COOL NOVEL MAKEUP AND KITCHEN 1,2,3,4,&5 Hayatu Baba Zubuiru (Ya Hayatu), daukacin masoya Novel din FuREN JUJI muna tayaka murnan zagayowar ranan haihuwar ka,🎂🎂🎂 Ubangiji Allah yasa albarka ga shekarun da aka diba, Babu shakka ka kai a yaba maka musanman ta yadda kake ilmantar da koyarwa uwa uba girki da kwaliya ga nishadantarwa mai karatu Allah ya kara daukaka da Basira 👏👏👏 Zaune suke su biyu suna karatu inda maryam ke koyawa Na,imat yin tsarki da kuma alwala a musulun ci, Maryam najin dadi sosai na yadda Na,imat keda saurin haddace karatun da suke yi, Sallaman mutyn kawai suka ji daga sama saboda duk basu san da zuwan shi ba a,yau din, Ku san lokaci guda sukai mai sannu da zuwa atare, Na imata mike da sauri daniyar zuwa ta rugun may shi kamar yadda suke yi ada in ya dawo daga tafiya, Da sauri Yusuf ya jaye gefe guda yana mai ce mata cikin kakasar murya I warn you is forbidden in islam pls don't do dis again, Cikin nuna jin nauyi Na,imat tai dan rau da fuska kamar mai jin ciwo, Maryam ce ta kawar da shirun da yadan biyo baya da fadin sannu da zuwa ya Yusuf, ya hanya, Daidai lokacin da yake zama ya karba mata da fadin Alhamdullah, Sai kuma yadan waiga kamar may nemar wani abu agidan Maryam ta mike a hankali ta tatara littafan da sukai amfani da shi, zuwa cikin wani dan loka da suke aje littafan addini aciki, Muryam shi taji yana cewa ina Anty ? A takaice tace sun tafi, gidan barka haihuwa, Fridge ta nufa da niyar dauko mai drinks amma sai taji muryan shi yana cewa, No, no,no iam ok, thanks, Mun tsaya Bobi gurin su mama an bamu fura da nono mun sha nagode, Da sauri maryam ta juya inda yake tana mai kallin mamaki don jin abin da yace, Cikin fuska ba sauki yace yes daga can muke tana gaishe kuma, Marfin fridge din maryam ta sake a hankali ta koma zuwa gefen kujerar ta zauna, Na,imat, wace ke kokarin zama kusa da shi take tambayar shi labarin maman Choima, Sai da ya dan furzan yace mama tana lafiya sai,dai fitina kawai data kara, maryam wace ke gefe guda tai murmushi, Sallamar mukaji daga kofa gida ko ba,a fada ba sun san cewa masu shigo da tsaraba Yusuf ne, Saidai wanan karon tsaraban ya sha bambam da na kullun, Wasu irin set din akwatina aka dinga shigowa da su, Mamaki karara ga fuskokin su maryam da Na,imat Da sauri maryam ta shimfida wani dan karamin center carpet a tsakiyar falo suka dinga ajewa a sama , Kafin wani dan lokaci duk sun gama shigo da abin da yazo da shi, Maryam batai mamaki sanin cewa yakanzo da motoci fiye da guda daya idan zai zo da wuya ya,shigo da guda garin, Shigowar Anty Dije gida,ne ya sa shi dakatarwa da dogon wayan da yake yi tun zaman shi acikin yaren su, Nan suka shiga gaisawa da ita tana mamakin ko ina yafito da wanan kayan, Bai mata wani bayani ba akai ya mike yana cewa zai tafi ya watsa ruwa sai yadawo, Fitar Yusuf Anty Dije ke tambayar mu ko kayan may ye wanan yazo da su, Maryam wace ke kokarin mikewa don shiga kitchen bata, tace komai ba don in ma har sanin ko na may ye ai itace ya kamata tasani, Tunda Yusuf yabar gidan bai dawo ba har suka gama duk wani aikin da yakamata suyi, Sai zuwa bayan sallah isha,i Yusuf ya shigo gidan, Wanda zuwa lokacin maryam ta fahinci Anty ta ta matsu tasan ko kayan may Yusuf yashigo gari da su, Don ita azaton ta kayan lefen shine yashigo da su tun da ba shi hakkuri a kai, Sun kara gaisawa da sister Dije inda take mai ya aiki ya bayan rabo, A hankali maryam tai magana kamar wace ke, jin ciwon baki, Tace mai a kawo maka abinci ne, Haba dai maryam wanan ai tayin rowa ne ko, Ina kin hada mai komai ko basai kawai ki kawo ba, Anya Maryam za muko, sha ruwa agidan ki kuwa tana wa Maryam din ba,a, Maryam ta dan turo baki gaba tace to anty idan kace zakaiwa mutum abu sai yace shi ai ya koshi, Ido kawai ya bita da shi yasan cewa don dazu zata bashi ruwa ne yace ya gode shine takewa wanan zancen, A bincin ta dauko mai har zuwa inda yake ta dora saman dan karamin stol, Ita da kan ta tai serving din shi da kuma kawo mai ruwa, Sai a lokacin ne ya fara yiwa anty bayani kamar haka, Anty ki samu time ki bude boxes din nan ki duba kiga abinda ke cikki, Idan da akwai abin da za,a saye akara sai ki fada min akaro, Maryam najin sun fara zancen akan akwatinan tai saurin mikewa daga gurin da take cikin niyae wuce wa ciki, Amma sai ji tayi anty na cewa maryam zo ki bude ke da Na,imat ku diba min pls, Ai bata san lokacin da ta dago kai ta kallo yae ta tace wa ni Anty,? A kwai wata maryam ce agidan bayan ke maryam, inji Anty, Kala batace ba sai wucewa da tayi direct gurin akwatinar, Da babban nasu daga ciki ta soma budewa don yafi tare guri, Zannuwa atamfa zube a ciki tankar shago, saida su kala,kala, Sai da gaban maryam ya fadi saboda irin kayan da aka jibga acikin akwatin Da aduke take sai takai tsugun ne saboda kafar ta ba zai iya daukanta ba, Haka tai ta daga kayan daya bayan daya har su ka kai karshe yana zaune bai ko kula da abinda sukeyi ba, Ànty angama inji maryam wace duk tagaji da dagawa, Wanan ai ba wanin abin da zamu kara aciki a kai masu haka kawai Allah dai yasa albar ka, Sai alokacin yadago yana kallon anty yace cikkn gyaran murya, Anty wanan kayan kayan auren Na,imat ce da Ibrahim, Wani ajiyan zuciya maryam tayi ta yadda ba wanda zai jita, Amma da fada takeyi don may zasu zageshi haka kuma ya wani zage ya kashe masu dukiya haka , Muryan shi ce taji yana cewa anty a,gaskiya , bana son Ibrahim yai komai anty, saboda ba wai yadade da fara aiki bane, Kayan daki nake son ki samu time sai aje azaba mata duk inda kikaga yafi, Cikin watan azumin nan nake son ko da an fara ne ayi auren pls, Saosai kowa ke kallon shi da mamaki yanzu duk wanan kayan ba akan shi ya sawa ba, Kawai don jin dadin wasu yayi shi, Shin anya kuwa ba zancen mutane gaskiya bane da suke cewa Yusuf wai furen kan juji, Don dai sam halaiyar shi duk abin ayabane baka taba ganin yayi wani abin assha, Bayan kuma mhaifin shi yana can a matsayin shi na kursungumin kafiri wanda ko da,wasa bsi kaunar yaji kalman musulunci, Sallamar wani yaron makwabtar su ne ya sa kowa shi, Yaron yace Assalamu Alaikum wai ance maryam ta zo ga A,A a waje gida, Wani irin fesar da iska Yusuf yayi da bakin shi don abin da yaji, Shi a,zaton shi Maryam basu tare da wanan guy din, Kanta ta maryam gefe cike da jin nauyi yadda yaron yai magana, Sai yanzu ta tuna cew tabar wayan ta a daki tun dazu tasan yakira lalayin ta bai shiga ba, Yaron zai kara sallama Anty Dije tai tsuki cikin tsawa tace wa yaro kai katafi dan Allah taji pls, Kamar may rada yadan kalli inda take yana nu mata kayan da yaci abinci Wani irin haushin maganar shi taji don tasan zai jagula mata al,amarin ta, Dakin tatakoma ta gyara kimtsawa alokacin yana zaune da Anty suna zancen uren, Cikkin shigar wani jan dogon riga ta material, anyi mata wani dinki mai shara,shara, Sai kamshi ke tashi a duk inda ta gilma saboda yadda ta daba shi a jikkn ta kamar da gaiyya Fitar maryam ba ai wani dade ba Yusuf yafito a kasalance, Hango su yayi zaune a cikin mota saida maryam kamar kullun kafar ta a waje yake ganganjikin ta aciki,wani irin haushi guy din ya bashi yau amma bai san ko may yasa ba, Maryam dake a cikin mota ta hango fitowar Yusuf din daga cikin gidan Full light ya sakar masu yana kallon yadda maryam take kokarin kare hasken motar da hannun ta Wani irin ashar A,A ya afka mai da ita wanda har sai da maryam tace, haba malam wanan zagi haka kamar yaro, Kallon ta yayi cikin nuna zargi yace, Maryam ku, kuka dauki wanan dan IBO da wani muhinmanci, IBO ne fa ba wata tsiya ba, ni wallahi zanyi maganin shi idan har ya shiga gona ta, Hannu Maryam tadaga mai abin da bata taba yi mai ba Tace shi IBO ba musulumi ba ne? Damay mutun ke nunawa agurin Allah da al,umma ban da Islama, Shi wanan da kake nu cewa IBO ne naga yafi wasu dubun hauwa( tauhidi) Ashe ke nan da ibo da bahaushe da bayerabe kai dama kowani irin kabila Mafi karfin imani shine mai rin jaye ga alumma bawai yare ba, Yadda kake ganin shi IBO anan haka acan kasar su suke ganin ka bahaushe kai ma Kallon ta kawai yake galala don yadda ta zake take kare Yusuf yau a gaban shi abin ya bashi mamaki, Sai dai duk maganar da ta fada babu wanda ba gaskiya ba daga cikki Hiran nasu daga karshe haka suka watse ba wani kwakawaran zance sai debet akan IBO da hausawa Ida ita maryam ta dage da cewa kabila bashine abin suka ga mutun wanda yake musullumi ba, Dane a lokacin da ake da karancin addini ake irin wanan maganar, Washe gari Yusuf bai shigo gidan ba sai kusan shadayan rana, Sanin yana gari maryam bata zama da kananin kaya agida kamar yadda idan mijin Antyn idan yana gari bata wani damuwa da gyaran jikinta, Yauma dai wasu zanin tamfane masu ruwan powder sai wa su flowers da akai masu masu ruwan milk, Zaune take a gaban tebur tana cin abinci a cikin natsuwa kamar ko , yaushe, Yakai wani lokaci agurin tsaye yana kallon yadda take komai nata a natse Sam bata da hayani ko wani rawan kai irin na yan matan da yake yawan gani, Ita dai gatan ako da yaushe sai umurnin da akaba ta arayuwan ta duk, da irin, halin miskilancin da ke gare ta kafin a saba da ita, Alamar tsayuwar mutum a kanta taji da kuma kamshi da bawai na irin turaren da yasaba sawa bane yau a jukin shi, Saye yake da wata yar farar tee-shirt, mai wani dan flower ja agaban rigar daidai saman aljihun gaba, Wani wando ne baki kamar Jens a wanan yadi yana wani dan walkiya, Cikin dan rudewa ko razana da ganin shi a tsaye tayi Saboda azaton ta har yazo ya karya ya wuce ko Sai idon ta ya hango mata abin karin sa a gefe aje, Don sam yau kin fitowa tayi tai kwanciyar ta kawai, abinta, adaki sai da ta ga cewa rana yayi shine ta fito, Da yar murmushin shi ya karaso har inda take zaune, Ina kwana ta tare shi dashi yayin da yazo gab da ita, Dukawa yayi gab da ita batare da ya amsa gaisuwar ta ba yace Saurayinki maryam baida kirki ga fahinta na bai dace yazo har kofan gidan ku ya saki a mota ba, mutane shiya suna ganin ku, Gaba kura baya karen daji, Jiya ta yi da A,A yau kuma Yusuf ya,tare ta da zancen A, A din, Ki kula maryam ke mace ce kada ya bata maki record din ki pls, Bata son nuna mai maganganun da yai mata sunyi mata tasiri a zuciya , Amma afili sai ta dake tace ban ga abin sa ido irin haka ba har zargi na son ya shiga, Yan mata nawa suke hira a mota wasu ma har gida suke bin namiji amma sai mu da muka zauna akofa za a wani sa muna ido, Wani ajiyar zuciya ya sauke gami da dan kura mata ido kamar zuwa second minutes, Mikewa yayi daniyar wucewa amma sai yaji muryan ta a rau,nane tana cewa "Na, Gode" Da dan mamaki ya waigo ta saidai kanta na kasa tana wasa da spoon din dake a hannun ta, Dan nazarin ta yayi sai yaji wani irin tausayin ta ya kamashi a take ya juya da niyar barin falon, Ga abincin ka can fa inji Naimat wace duk basu san cewa ta na gurin ba ashe, Hannu yadaga mata alamar yagode kawai ya juya yabar falon, Kallon mamaki da al,ajabi kawai maryam kewa yusuf din Ita ko Na,imat saida ya fita tasa hannu ta toshe bakin ta tana darita cikki,cikki tace Wa maryam da gani nasan cewa kin tabo big brother yau, Maryam tace kawai dai yaso yasa wa kanshi abin da bai shafe shi bane, Nan dai maryam ke fadawa Na,imat yadda sukayi da shi, Na,imat tace gaskiya sister ba karya bane don mu yaren mu bamu irin wanan sam, Kinga kuwa tunda yanzu anzama daya dole ya fada maki gaskiya, saboda yasan cewa zubar da mutunci ne irin haka, Mamakin jin abinda Naimat tafadi maryam tayi, Yanzu a she har akwai abi da bahaushe zaiyi ace wai IBO naganin shi a cikin rashi tarbiya,,,,,,,,,, ZEEE MAKAWA [3/24, 10:10 PM] Zainab Makawa: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, Kaunar da kuke nu na min yasa har na kasa bakin godiya agare ku, Fatan Alheri ga duk wance ta fahinci ma,anar wanan sakon da nake isarwa, Ubangiji Allah ya kara maki ke mai karatawa daraja da,dauka, Allah yasa mu gama da duniya lafiya baki dayan mu Allah ubangiji ya taimaki addini musulunci da ma musulman baki daya Ya Allah karawa Annabi Daraja,👏👏👏👏👏 Gudu yake shararawa acikin motar shi hannu shi guda yana, dan shafo fuskan shi dashi a hankali, Tunane yakeyi wai may ke sa shi damuwa da al,amarin wanan yatiyar ne, Har raini yana son shiga a tsakanin su don tafara mayar mai da magana mai zafi, Tsuki yaja yace why tausayi zai ja mai raini a gurin ta, Zai yi kokari ya killance kan shi daga harkokin ta bazai kara sa mata ido ba, Tun bayan barin shi gidan bai shigo ba har sai zuwa misalin hudu na yamma, Lokacin duk sun kare aiyukan da Anty Dije tabar ma,su yi,,, Saidai fuskan shi kawai zaka kalla kasan bai a cikin good mood yau din, saboda yadda idon shi suka kada sukayi jajir da su, Kallo guda tai mai tunda ya shigo ta kauda kanta daga ganin shi A take wani yanayi maikama da zazabi ya sauka mata, sai taji kawai kwanci take so a lokacin, A kan gado ta zube sannan ta lumshe idanun ta a hankali a sannu take jin yadda zuciyar ta ke bugawa, Muryam Na,imat ce a kanta tana cewa Maryam lafiya ki ka kwanta by dis hours, Kwanci bayan dis hours yana kawo wa mutum zazzabi fa, Ido a lumshe ta ansa mata da fadin lafiya kalau, nadai dan kwanta ne kawai, Dafata tayi tana cewa to ki tashi wanda kika kwanta don shi shima ya wuce bai tsaya ba tunda yaga jeloup din taliya mukayi, Cikin wani hanzari tamike zaune dan jin cewa bai ci ba ya wuce, Tambayar Naimat tayi cikin damu to may zai ci da ya wuce,? Aida kin tambaya ko da abin da yake so ai mai ko,? Kin san halin brother baya son dogon magana shi yasa kawai na kyale shi, KB yana gari don haka yana fita ya juya akalar motar shi zuwa gidan, Wayar shi ce alamar kira ya,shigo mai a lokacin, MARYAM BLACK, Yagani a rubuce kamar yadda yai serving din sunan ta, Cikin hanzari ya mija hannu yadauki wayan adai,dai lokacin da ya tsaida motar shi,kofar gidan KB, Da sallama yadauki wayan yana cewa maryam ya dai ? Kafin ta ce wani abu sai tai dan shiru saboda Naimat da ta tsure ta da ido, A ladabce tace Ya Yusuf baka ci abinci ba kawuce, Murmushi yayi dan jin dadin kula shi da tayi, yace No bana cin taliya ne yanzu shi yasa To amma shine bakai magana ba sai aima wani abin, No, no no ki barshi kawai zan sha drinks ai, Wani ajiyan zuciya tayi har sai da yaji ta acikin wayar, Sallama taimai inda yake ce mata yagode cikin wani murya maikama da na tausayi, Jingine wayan tayi a saman kirjin ta , tana tunanen irin saukin halin Yusuf din, Yanzu ya shigo fuska murtuk kamar an aiko mai da sakon mutuwa amma sai gashi taji muryan shi kuma yanzu normal, A gidan KB Yusuf a waje yake tsayawa saboda baya son irin yanayin matar KB din, Don ita ko maza sunkai nawane zata iya zama acikin su, Ko kuma takama gittawa a gaban su cikin shigar matsatun kaya, Shikuma hakan ke sa yana kare idon shi da daukar dumbin zubi, Duk yadda KB yaso su shiga Yusuf yaki sai da KB din yace mai ai ba kowa sun tafi gidan su gurin bukin aure,, Ya,samu akwai abinci da aka zubawa KB din shi ya dan ci amma kadan saboda bai ji test din abincin ba, sosai, A lokacin da yakora ruwan mai sanyi da KB din ya dauko mai acikin fridge KB din ne yadan dube shi yace wai ya ake ciki ne akan zancen ku da yariyar nan ne, Ina sa zuwa yanzu har anyi engagement sai kuma na shiru kawai Man ya kamata fa ka maida hankali ka aje iyali zuwa yanzu, A je roban ruwan yayi a saman tebur din gaban shi ya ce, Ai kasan komai a sannu akeyin shi idan time yayi ba,wani bata lokaci ,sai ayi, KB yace gaskiya ne ba shakka haka maganar take aure dan lokaci ne, Washegari duk kan su gidan gyaran jiki sosai akai masu, Daga adon lalle da kuma dilka, sai kuma kitso da aka yarfa ma su gwanin ban sha,awa, Gaba dayan su sun fito shar da su, duk wanan shirye, shiryan sunan da za,a yi ne na haihuwar kaunar mijin Anty Dije da tayi, Ita kanta maryam tasan cewa sun yi kyau duk da ita ba ma,abociya son yin kitso bane, Allah ya tai make su har aka gama masu Yusuf bai shigo ba saboda yar tafiyan da yayi zuwa kauye, Da sallama ya shigo gidan inda ya fara cin karo da Na,imat wace a yanzu duk ta juye ta zama bahausa sat, Saida gaban shi ya fadi irin yadda yaga ta koma alokaci guda kai Musulunci ma Rahamace ya furta a cikin ran shi shi kadai, Anty Dije ce cikin shigar wasu dinkin Senegal's da mijin ta yasayo mata da sallah bara, Da fara,ar ta a fuskan ta ta shigo falon gurin Yusuf, din tana tambayar inda ya tafi,jiya, Maryam najin shi daga dakin su amma sai taki fitowa su gaisa, Duk hiran da suke yi da Anty Dije sai ya tsunci kan shi da rashin jin dadin ganin maryam din kamar ya tambaya ina ta ke sai dai ya daure, SAFIYA ce ta shigo gidan da sallamar ta Anty Dije wace ke kokarin aje cup din da tasaha kunu a saman tebur ta dago kai tana amsa da yar fara,ar ta a fuskan ta, Da murmushi makale a fuskan ita Safiya ta zauna saman daya daga cikin kujerar falon suka gaisa, Sanan take tambayar maryam din Anty Dije tace barin kira maki ita tana can dakin kusa da kitchen kwance, Lokacin da Anty ke shirin mikewa ita a lokacin maryam ta shigo falon da murrmushi makale a fuskan ta, Wani irin mugun shock yaji da yana cewa Naimat ta canza cikin dan lokaci sai ga kuma maryam kamar wata Amaryan wani gwauna, Da sauri ya kauda idon shi gare ta da ya daga don amsa mata sallamanta, Safiya ce ta tare ta da cewa ke wanan irin haduwa fa kamar wata, amarya can, Hararan ta maryam tayi tace ina kwana Ya Yusuf, kamar bai gurin Amsawa, yayi batare da daga kai ba Safiya taci gaba da cewa Anty shiya sa Dan iskan ga ya wani leke mata kamar kaska, Ni wallahi Anty A A din nan Allah yakawo wanda zai kifar da gwaunatin shi a zuciyar maryam, Dan takaitaccen murmushi Anty Dije tayi tace, Wanan ai tai nisa Safiya indan kin ce ba shi ba yanzu zaku bata ne, Cikin daure fuska maryam tace wa safiya, gaskiya ke sai mun hau sama dake tukun ina ga zamuyi daidai, Ta juya tai hanyar shiga dakin su tana magana kasa,kasa, Safiya ta juya tana fuskantar Anty Dije tace wallahi, anty bana son zan cen wanan mutumin sam mugune har na karshe, Nan dai sukai ta zance a kan A, A din har zuwa dan wani lokaci, Yusuf wanda kan shi ke a duke yana ta faman dadannar wayar shi bai ce masu uffan ba, Daga karshe rai a bace Anty Dije ke cewa, ai duk abin da zai mata Allah bai bashi ikon cutar da ita, Maryam tafito cikin shigar wasu kaya kamar les a jikin ta sai dai ba masu nauyi bane su tai wani irin bala,in kyau, Naimat ce a bayan ta ita cikin shigar wasu kaya da Yusuf ya dinko mata, A tare zasu tafi gidan kaunar mijin anty dije inda ake suna, Ga kayan ci da na sha nan kala kala da suka dafa da,soyawa wanda za,a tafi mata dasu, Ganin yau gidan da taron mata yasa Yusuf mikewa yana ma Anty sallama, Yusuf don Allah ko yan matan nan ka fara sauke min su a gidan bukin pls, Daga kai yayi ya dan kalli gefen da suke idon shi caraf a cikin na Maryam, Da sauri maryam din takawar da kanta gefe guda cikjn sauri, Amsawa Anty Dije yayi da to badon yaso ba, a haka aka dinga loda kayan da zasu tafi dashi a cikin motar shi, A hankali suke tafe inda yau kidan turanci ne ke tashi a cikin motar shi, ga sanyi AC da ke ratsa masu jiki a hankali maryam ke bin wakar da ke tashi a cikin motar,, le me love you, ,don't give up , i won't, give up, now, know, know, Kusan duk wakan suke bi, a motar inda Naimat ta kawar da dan shirun da ya biyo baya, Tambayar shi tayi ya zancen shi da Sadiya ne wai an gyara kuwa? Bai bata ansa ba sai ma jefo mata tambayar da yayi cewa tana bukatar tace, tazama cikin su, Kafin Naimat tai magana. Safiya ce tace mai wai, haryanzu zancen yana nan ashe ? Naimat tace nafison brother ya samu mata wace zata iya kula da mu yan uwan shi a duk irin halin, yadda muke, Kin san fa mu a yaren mu mace ce ke kara karfafa zumunci ba namiji ba,,, Idan munzo gidan shi ba,a tare mu da fuska mai kyau ba ya zamuyi Kinga ke nan zumunci ya baci saboda ita mace ita ce mai zama gida, Tunda Naimat tafars magana ba wanda yace mata komai har ta kai aya, Bayan ya sauke har zai wuce sai Naimat tace dan Allah brother ba dadewa zamuyi ba , A,lokacin har su maryam sun fara tafiya, zuwa cikin gidan bukin , Safiyane amma kasan cewar haihuwan fari ne gida tab yake da jama,a daga fanin mijin ta har na,ta da abokan arzikin, ta, Bayan sun gama shigar da kayan da,suka fara zuwa dasune a ciki, Sai suka samu gefe guda saman fararen roba dake karkashin wani runfa suka zauna, A daidao inda suke zaune akwai mata gun,gun a zazaune saman fararen kujerun roba, Wa su, kujeru da wasu matasan mata suke zaune akai su uku sai kallon inda su maryam suke suna kus,kus, Sai leken su maryam akeyi, tun farko maryam ta halkanta da su amma sai ta shere su don gudun zargi, Amma kawai sai daya daga cikin matan ta tasao har inda suke, zaunr tace, wai kamar Ejoma wanan ko ? Safiya ce tai carf tace Naimat dai ko, ? Matar tana murmushi tace gaskiya kamar su yai yawa sosai , Naimat tace nice da sauri ta waiga gurin da yan uwan ta suke zaune tace, Itace bana fada maku ita bace, ashe kin musulunta ne, Safiya tace haba tunda har kin ga zahiri may ye na tambaya pls, Ke ko yar uwa don ance mata tubabba shine wani abu, Haba amma hakan ya zama tozarci ko tunda har mutun ya riga ya zama musulumi, Sai gudan tace to am a ai don an tuba ba a taba cewa batai zama kafira ba ada, Innalillahi, maryam tace cikkn nuna bacin rai ga matan, Haba dai Anty Rukkaiya ai wanan bai dace ba ga addini ko ? Safiya tace ga wanda yasan addini ke nan maryam Wai mutane sai su manta da cewa da wanda yai shekara dubu da wanda ya shigo yau fuk guda suke ga Allah, Har ma wanda ya shigo yau idan ya rike addini saima ya fika don shi baida zubi tukun yana tare da gafaran ubangijin shi, Haka abin yaso yazama kamar fada a,tsakanin su don Safiya ta dauki zancen da zafi, Su basu ko farga cewa Naimat ma bata gurin ba tunda taga irin yadda abin ya zama tozarci ta sulale ta fita kofar gida, Sai da wasu manyan su suke tambaya wai akan wace,ce ake zancen Safiya taje ta nuna Naimat taga babu kowa aguri , Da mamaki take kallo. Maryam tana tamba yar ta cewa ina Naimat din take, Mikewa su kayi a,lokacin da ake cewa matan basu da gaskiya Su daina yiwa mutun tozarci irin haka saboda hakan yazama cin fuska,, Naimat wace ta koma can kofar shigowa gidan tai zaune cikin bacin rai, Shigowar Anty Dije ce yasa tadan yi kamar ta sake, fuska, Tambayar ta Anty ke yi ko may yasa ta fito waje, ina kuma su Maryam da Safiya, A wanan lokacin suma suka i,so gurin suna neman ta ta, Ko ba,a fada ma mutum ba yasan cewa a cikin bacin rai take kawai, Safiya ce tai kokarin yiwa Anty bayani kamar yadda akayi da matan Cikin bacin rai anty ke cewa su tsaya ta samu wanda zai maida su gida, Sai yanzu take, da ta sani tabar su agida kamar yadda su ka bukata tun farko, Cewa su bazasu zo ba za su zauna gida kawai har ta dawo ita da yara amma sai tace tun da buki yaune kawai su tafi tare kawai, yafi, shine har maryam ta gai,yato safiya don su tafi tare, Zaune yake jikin shi duk kamar ba nashi ba Naimat tana ta labarta mai abinda ya faru, Sai hawaye take ta zubar wa tana ta kokarin share hawayen da ya zubo mata a fuska da gyalen da ta yafa ajikin ta, Maryam tana tsaye gefe guda tabi lafiyan bango tana sauraren yadda yake bata hakkuri, Wani irin tausayin su take jin ya kama ta a lokaci Batasan cewa hawaye na biyo mata fuska ba har sai da taji mutum tsaye gab da ita Ta yadda bazata iya ko da motsawa ba handky ya mika ma ta batare dayi mata magana ba, Girgiza kai tayi alamar aa ya barshi kawai yana kallo tasa habar hannun ta ta goge hawayen Ko karin wucewa take yi zuwa ciki a lokacin batare da tace mai uffan ba, Sai dai babu hanyar da zata bi ta wuce ko ka dan ga kamshin shi da ya cika mata hanci kamar kamfanin turaren, May ki,ke,wa kuka maryam kifada min dan Allah ZEEE SEENABU MAKAWA [3/28, 9:00 AM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA IYAKA, NA,ABBUD WA,IYAKA NASTA,IN,,👏👏👏👏👏👏👏👏 Tsaye yake a tsakiyan falon gidan shi daga shi sai singlet da wandon shi dogo dake jikin tun da rana, Safa da marwa yake yi a,cikin falon, a inda ya goya hannayen shi a bayan shi, Komawa yayi yadan jingina bayan shi da bango kadan, Yadan daga kafar shi guda ya dage a bayan bangon, Da sauri ansar da tunanen shi ya bashi akai yai sauri girgiza kai tankar da wani yake magana alokacin, Ina sam ba gaskiya bane sam sam yariyar da bata ko kai Ruth shekaru ba, Ina sam wanan zancen banza ne may zan so gurun maryam, Ko shi saurayin nata ai kawai rigimar tane ya kai ta amma ai da,sauran ta, kawai dai don tayi saurin fara karatu ne kamar yadda yaran hausawa ke saurin shiga makaranta, Tsuki mai tsawo yaja batare da ci gaba da tunanen ba ya juya zuwa bedroom din shi, Hakan ya fada saman gadon shi batare da tsayawa sauya kaya jikin shi ba Sai cikin dare daidai lokacin da ya,saba tashi don yin kiyamallaini ya mike zuwa bathroom, A gurin da yai sallah asuba yana lazumi nan barci ya kara daukan shi mai tsawo, Wani mafarki ne yadan dauke shi zuwa duniyar mafarkai, Tafe yake yana rike da hannun wata, mace wace, ke dauke da tsohon ciki a jikin ta Tafiya matar keyi da kyat tana faman ciji baki don wahala, Iya tausayi matar ta bashi hakan ne yasa shi zuwa ya dan taimaka mata,, Dukawa tayi don wani irin azaban zafi da ya ziyarce ta, da sauri ta fisge hannun ta gare shi, Ta dan kai wani lokaci agurin duke tana fama da murdan ciki, Sannan matar ta dago fuskan ta da yaga ni shi yasa shi ja da baya cikin wani irin mamaki Sai kokarin nunata da yatsa yake saboda bai san cewa itaba ce ke wanan wahalar, Juyawa yayi daga inda yake a kwance,, daga haka sai yabar wancan mafarkin na farko, Wani mafarkin kuma shiga yi inda yake tsaye yana tura wata yar matashiyar budurwa a saman wani lilo A,hankali yake tura ta inda kanta yake duke, sannu a hankali ta dago kai zuwa saman kirkin shi ta kwantar da kai Sun dauki tsowon lokaci a haka da ita sai dai sam baya iya ganin fuskan ta, Ya kai wani lokaci agurin yana kwance a kasa saman carpet yana barci, Zuwa yanzu tun bayan musuluntar shi yasaba da irin wanan kwanciyar a saman abin sallah shi idan ka gan shi ya dunkule guri guda zaka,zaci cewa ba shi bane, À yadda zaka ganshi matashi dan kwalisa mai i,limin zamani kuma ga naira ta zauna zaka zaci cewa ba zaiyi jimirin jurewa yin ibada ba Badon komai ba kuma sai,don za,a iya cewa haye yayiwa addinin a sama , Ba zai iya rike ta da kyau kamar yadda yakeyi a yanzu ba, Karan wayan shi ce ta tashe shi daga barcin da ya samu mai dadi barcin safe ke nan, Idon shi a rufe saboda dadin barcin ya mika hannu dai,dai inda karar wayan nashi yake fitowa, ya dauko ta cikin kasala, Antonia ya gani rubuce, zubur ya mike don kiran da yagani daga NANI ANTONIA, Hlo, how you na dey, Batare da ta ansa mai ba,take cewa Oga Pipkin dey sick since yesterday, E no even go to school woo, Mikewa yayi zubur yace subbahanallah, gami da furta sunan dan yaron, Abdulraham a fili, tare da kokarin mikewa tsaye, daga gurin da yake kwancen,, Hlo, Antonia yace cikin harshen turancin yan kudu, Ki shirya, shi kun ji zan kira doctor yazo ya diba min shi yanzun nan pls, Yana kashewa ya shiga neman nobar doctor chukuma,, Doctor chukuma wani likitan yarane da yake yawan kai yaron gurin shi tun bayan dawowar su Abuja, Ba wani bata lokaci ya kira doctor din ,wanda a kira na farko ya, samu nobar doctor din a gurguje yai mai bayani cewa ya je gidan shi ya diba mai boy bai,da lafiya,, Wanka yafada saboda ya samu ya isa Abuja da wuri ranan Sai alokacin yake mamakin irin wanan gwaunatin ta Nigeria, Ace babban gari mai tsohon tarihi kamar garin kwantagora , Wacce ta tara din,bin al,umma iri,iri wai har yanzu ba ai mata wani abin cigaban al,umma kasar ba, Ya kamata ace yadda take business center tana da hanyoyin masu sauki daga railway ,zuwa airport, da sauran su, Amma saboda handama manyan kasar mu da basu da kishin zuci har yanzu an rasa wanda zai yiwa wanan kasar irin wanan aikin cigaban, na al,umma, A cikin barci da sukeyi na safe mai dadi da shiga rai suke jin muryan Yusuf din sama, sama, A hankali ta bude idon ta a dai,dai lokacin da takejin yana cewa anty yanzu zan tafi Abuja don an bugo min waya yau da safe cewa, Pipkin bai da lafiya,, Kuma yaron bawai ya wani saba da sabuwar nani din shi ba,ne, Don kusan zuwan Naimat, nan ne na dauko matar daga kauyen mu,daga haka sai, A hankali kuma taji dan she,shekar kukan Naimat a bayan ta, Cikin idon barci maryam ke kallon Naimat din inda a hankali tadan mike zaune, Inda Naimat take zaune take kallon ta, wacce ke kokarin goge hawayen dake sin,tiri a idon ta, Ganin maryam din ta farka,ne yasa ta juyowa inda take zaune suna fuskantar junan su, Hannun maryam tariki a cikin kuka ta nace wa maryam din, Maryam ina son yaron nan, bana son ya mutu wallahi, Saboda na,sha wahala sosai akan shi zaman da, da ,ni akwai wasu muhinman abubuwa da nake tunawa, akai, Maryam wace ido kwai ta kura mata a cikkin mamaki, take kallon, Naimat din don sam bata fahinci inda maganar ta ya dosa ba, Sai kuma hankalin ta ya,koma falo su, inda taji Anty Dije na cewa bazan bari kabi hanya baka karya ba Yusuf kabari ko cooker,oth ne a, dan dama ma,ka Daga Saman gadon tai ko,karin saukowa a lokacin kafin ta idda sauka taji muryan Anty cikin daga murya tana kiran ta, Sam ta mance cewa kayan barci ne ajikin ta don haka ta nufo falon da sauri, Riga da wandon kayan barci sabon kitson da akai mata na wevin "yan ritsi,ritsi, sunyi lub, lub a kanta , gwanin sha,awa, Da sauri ta iso inda anty ke tsaye dauke da yaron ta, Shi ko sarkin lakewa a jikin uwar shi, a hannnu, ta yake dauke yana son shan nono, yanzu Itama Anty sai yanzu tasan cewa kiran da tai,ta kwadawa Maryam din yasa ta rudewa cikin barci ta fito a haka, Zanin da ta jawo don ta dan daura a sama take kokarin daurawa akai tana fadin gani Anty, Da sauri ya kara waro idon shi waje don sak kalan kayan da yaga mai cikin da yai mafarki ne dasu da asuba, Don Allah hada heater ki dama wa Yusuf cookeroth da,sauri pls, inji Anty Dije, Sai a lokacin maryam wace tagama daura zani saman kayan barci ta, ta kai kallon ta inda yake tsaye tace , Ina kwana a hankali, Shima dai ansa mata yayi cikin rashin walwala da sauri maryam ta nufi hanyar zuwa kitchen, din Wani irin mugun bugun zuciya yaji mafarkin ne ya fado mai a ran shi, Kafin yan mintina har ta hado mai cikin wani bowl mai dan fadi tazubo mai saboda yai saurin shan iska, Anty Dije ce tace dan juya mai ya sha iska don Allah kada ya makara,, Fuskan shi a hade kamar wanda bai taba dariya ba a rayuwan shi, Wai waye Pipkin din nan ta ke tambaya a cikin zuciyar ta, Dukawa tayi daniyar tafara motsawa mai orth din, Wani kamshi ya daki hancin shi wanda saida yadan kara kallon ta ta wutsiyar ido, Mamaki yaji don yasan daga barci ta tashi tafito amma kuma take wanan kamshin haka ? Kai wanan yariyar akwai tsabta da yawa idon shi ne ke kallon yadda har an gyara ko ina na gidan ko kamar ba,a bata ba, Muryan maryan ce mai magana cikin sanyi take cewa Ya Yusuf addu,an samun lafiya za ai mai kasan ciwo bautan Allah ne both babba da yaro, Amma duk da haka akwai wasu magani da mukewa yara amfani da su sai ka tafi mai dasu adinga mai amfani dashi a gani, Mikewa tayi don ganin kunun yai dan sanyi saboda tasan cewa baya shan abu mai sanyi shi, Dakin Anty ta shiga sai gata tafito da kwalaben magani a hannun ta, Kara durkusawa tayi gaban shi tana mai bayani guda guda yana dan kurba kunun dake a hannun shi vikin cup a hankali, Idon shine suka sauka a gaban rigar barcin ta waiyazu ;billah Da sauri yakau da kan shi gefe har takare mai bayanin cewa wanan man Habbatussauda ce, wanan, Zaitun ne, sai kuma man Albasa a dinga hadawa da pure zuma, Takare maganar nata da ce wa a hankali Allah ya bashi lafiya, Ameen ya ce cikin jin dadi da irin nuna kulawar da tai mai, Sai alokacin ta juya gurin da Anty Dije take zaune tana shayar da danta tace Anty idan zan fita atuna min in sayo wasu a aje dan Allah, Mamaki yaji cewa sayen maganin ma sukayi ashe, Bai wani dauki lokaci ba ya mike yana kokarin gyara jikin shi inda yadan takure, Naimat ce tafito, cikin damuwa duk da tayi na mijin kokari gurin saita kan ta saboda kada agane cewa tayi kuka, Maryam wace ke tambayar Naimat a cikin kashe murya, Pipkin din yaron waye shi ? Murmushi kawai Naimat tai mata, batare da taba ta ansa ba, Ànty Dije ce tace ke baki san yaron Naimat ba Abdulrahaman, Wani irin kallon mamaki maryam kewa Naimat daga haka Yusuf yai masu sallama ya tafi, Yusuf tuki yakeyi shi kadai a cikin mota sai sharara gudu ya ke yi, A cikin nishadi yake tukin shi hankali kwance sai dai kuma zuciyar shi tana gurin da yake, tunane Sai,dai a kai, akai, yana dan duba agogon hannun shi, sai kuma ya daga kai yadubi, hanya, A gaskiya a yadda ya samu yaron yana jin jiki sosai, Saboda duk da ya samu yana barci amma jikin shi gadau yake da zafi, A hankali ya duka a gaban yaron yana mai dan taba mai jiki a hankali,, Wayar shi ce tai kara alamar kira ya shigo mai, a lokacin, Batare da ya mike ba daga inda yake yadauki wayan MARYAM BLACK yagani a rubuce wani irin murmushi ne yadan subuce mai, Assalamu Alaikum, tace cikin yar siririyar muryan ta, Ansa mata yayi da wa,alaikissalam , Maryam na barku lafiya, Ya Yusuf ya hanya ka kusa isa ko, Ina gida Maryam, Yana jin ta tana cewa yai har ya isa fa,? Muryan anty yaji tana cewa Yusuf wallahi ka rage wanan yawan gudun naka fa, Maryam ya ambaci sunan ta, cikin wani irin murya, Naam ta ansa mai itama cikin rudewa da jin irin kiran da yai mata, Ya maijikin tace mai cikin sanyin murya, Nasamu yana barci, amma dai jikin shi da zafi sosai wallahi, Ya Yusuf kasamu kyale ko towel, kasa a ruwa ka din ga tai maka mai, dashi kana dan goge mai jiki dashi, Jikin zai mai sauki idan an gama saika bashi wanan man albasan da sauran su ya sha, Sai kuma tai shiru bata kara cewa komai ba daga hakan jun shirun nasu yai yawa shiyasa yakatse da,cewa abashi Anty, Zaune yake a bakin gadon da ruwa da wani farin towel, A hankali ya ke matse ruwan da towel din ya kwaso, Yana dan mannawa a jikin yaron dake kwance a saman gadon shi, Nani Antonia ta na tsaye gefe guda ta dan rakube a bango tana kallon abin da yadace ace itace tayi amma sam rudewa ya hana ta yi tun farko, don da ace tayi da jikin yaron bai kai haka ba, Sannu a hankalo ya bude idon shi ,ba su sauka ko ina ba sai a,saman fuskan Uncle din shi, A hankali ya ce uncle, sai kuma yai dan murmushi, Wani irin tausayin yaron nen ya kama shi yaro mai kyau ga wayo amma ace wai ya tashi babu uba, Kai mutane ba su da tsoron Allah sam, ka haifi yaro sai kuma kaki shi, Yanzu badon Allah ya nufi yaron da,zama gurin shi ba da haka zai tashi acikin addinin Christian, Uncle yaron yace a lokacin da yake kokarin ganin cewa ya kai zaune, Da sauri Yusuf yatare da hannun a haka yadan mike zaune yana dogare da bayan hannun Yusuf,din Rugumay shi yayi a lokacin maman Choima ta shigo dakin da cikin tafiya irin na tsofi Da harshen IBO take mai yadawo lafiya ya hanya,saboda bata san inda ya tafi ba,, Nan take ce mai wai yaushe ne Ejoma zata dawo garin su da ta tafi, Ita fa shiya sa tace, tun farko Ejoma taje da dan ta, Gashi yanzun ta wuce tabar mutane da yaro ana mata wahala, Kan shi na duke yana sauraren ta yana makale da yaron a jikin shi, Yace Mama,aaa,,,,,mamaaaa will stop dis, Abdul is my son pls, Lokacin yaji dan yaron ya kara shige mai a jikin shi ,shima dai din kara rungumay yaron ya yi cikin jikin shi, Sai da ya tab batar da cewa yaron yaci abinci ya koshi san nan yasa akai mai wanka ya kara bashi magani, Zaune a bakin gadon shi yana kallon wayar shisai dai ji yakeyi kamar ya kira maryam a lokacin, Saboda irin yadda yake jin kewar ganin ta a yau din, A hankali ya maida idon shi ya lumshe ya fadi a fili she is beautiful, And her skin is natural, Kwance yakai ta baya saman mamakeken gadon shi yace And very religious, wayan shi ce tai kara azaton shi maryam ce amma sai yaga Aisha, ce, ke kiran shi, Aisha ya kara furtawa yau rabon da ta kira ahi tun lokacin da sukayi sa,in sa da ita akan sadiya, Baikara kula ta ba ko yanzu kamar kada ya dauka amma sai ya daure yadauka,, Sun yi gaisuwa na mutunci da shi sai kuma ta fara mai korafin wai ya shigo KG yaki neman ta har yadawo, Zata ci gaba da magana yadakatar da ita da cewa Aisha na fada maki ba yauba cewa baza mu shirya ba, Saboda duk halaiyan ki basuyi min ba san kwata,kwata bana son inga mace bata kamun kan ta, Nayi dake ki daina amma kin kiya,,,,,,,,,, SEENABU ZEEE MAKAWA [3/28, 9:01 AM] 0mmer Farouk: .🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA IYA,KA, NA,ABBUD, WA IYA,KA,NAS,TA,INN Zaune take tana kokarin shiga barci amma hankalin ga na gurin dan yaron da taji an kira,sunan shi da Pipkin, din, Duk da ba sanin shi tayi ba amma tausayin shi ya, kama ta a cikin ran ta,, Kamar kullun yadda ta,saba kafin ta kwanta, barci al,adan tane ta zauna ta shafe jikin ta da kayan kamshi duk da ba,wasu masu tsada bane, Sai kuma takan zauna ta dinga jero adduoi da duk ya dace tayi kafin ta,kwanta, barcin, A hankali ta,shafa adduan karshe da tayi ta,juya dai,dai gefen daman ta, ta,kai kwance, Hannun ta ne ya sauka saman kan wayar ta kamar ta share sai kuma ta dauko wanyan, Nobar A, A din ta ne last call din ta na yau, sunyi magana da shi akan cewa zai yi tafiya na yan kwana ki Zai tafi su gana da mahaifiyar shi wace ke zaune Abuja da mijin ta da take aure yanzu yana aiki a,Agric Bank, Kamar ta aje ga kuma idon ta na kallo nobar Yusuf din, Inda Naimat take kwance takure saman kujerar three seaters wani irin tausayin Naimat din ne taji yakama ta, Don tun da labarin rashin lafiyan yaron yazo musu tun wanan lokacin Bata da wani kuzari ajikin ta duk ta wani su,su ce a yinin ranan, Direct takai hannun ta ta dan na kiran layin shi batare da wani tunane ba,, Yana a kwance idon shi a lumshe yana tunanen bari ya, shiga wanka ko zai samu natsuwa, Firgigit ya na kallon gurin da,wayar yake saboda tun gama wayar su da Aishan shi wace taita mai masifa akan rashin kulata da ya daina yi yan zu, Maryam Black yagani maryam again ? da sallaman shi ya ansa kiran nata, Cikin wata irin dasasshiyar murya yace maryam ya kuke ya su Anty da yara, Ta ansa mai cikin yar muryan nan nata da cewa lafiya, lau, Uncle ya yaro mai jiki yaji sauki ko,? Murmushi ya sake saboda jin yau ta tuna da tsohon sunan da suke kiran shi kafin ya musulun ta, Alhamdullahi don har ya ci abinci , Masha Allah maryam tace, Sai kuma tai shiru, Shima dai din shirun yayi a lokacin To Allah ya sauwaka, tana batun kashe wayan, Au maryam har zaki kashe wayan ke nan ban ko gama magana ta ba, Murmushi tayi tace kawai dai dama don muji cewa ya jikin yaron ne yasa na bugo ma, Ina Assalam ? Ta karba mai da cewa gashi nan yayi barci, tun dazun Cikin hikima ya rika dan janta da hira kadan kadan,, yana mata yan tambayoyi Sai kuma ya fada zancen Assalam da isalam, Duk dao don ta saki jikin ta da shi , Har zuwa wani dan lokaci mai tsawo maryam a zuviyar ta duk ta matsu ta aje wayan saboda duk a matse take tankar a gaban shi take magana, Duk da Yusuf ya fahinci cewa tana son anje wayan hakan bai sa ya kyale ta ba, Sai cewa da ya yi idan yaron yaji sauki zan dawo don ban gama abin da nake yi ba nadawo, Batare da tasan may yafito daga bakin ta ba sai cewa tayi, To ya Yusuf ka,zo, dashi mana nan gurin mu tunda mahaifiyar shi tana tare da mu, Idan nazo dashi may zaki iya yi mai, ? Yar dariya gun,tuwa tayi tace ni , ? Haba dai yaya Yusuf sai kace ni ba mace ba ce , "Masha, Allah" yace " Aishe mijinki ya huta ke nan tun da kin iya reno, Kar ki damu ai nan ma akwai, wace ke kula dashi sosai tankar uwar shi na kusa, Amma dai ai zaman shi a kusa da uwar shi ina ga zai fi mai ya sake ko,? Murmushin maganar da tayi yayi kawai saboda yadda tai maganar nata tankar, wata babban mace, da tasan yadda ake kula da yara, Kaga sai ka sallami Nani din nashi ko ? Wani sabon dariya yasa mata wanda dariyan yaba maryam mamaki so sai, Tambayar ta yayi, don ya ji a kage take da ta kashe wayan May yas naga kin damu da zancen ciwon Abdulrahaman, ne, Cike da jin kunya maryam tai yar murmushi tankar yana a gaban ta, A kunyace ta ansa mai da cewa saboda nasan cewa yaron na da muhin manci a gurin ku, Kuma dai ai yaro na kowane ko ? Murmushin da yayi har cikin dodon kunnen ta, taji shi a lokacin, Sallama sukayi inda yake mata godiya da kuma yimata sai da safe, Barci mai nauyi yai gaba da ita, bayan ta kashe wayan, Na imat wace ke lafe tankar wance tai nisa a cikin barci Tai wani irin ajiyar zuciya bayan ta gama sauraren duk yadda sukayi, Ita dai a rayuwar ta, wanan yariyar da yar ta sun mata wallahi Babu ruwan su sam su duk yadda mutum yake basu kyamar shi ne ko ? Ba kamar sauran ba, Juyawa tayi ita ma tai adduan da maryam ta koya mata na barci, Kusan satin shi hudu a can sanan yazo garin su inda zai gana da iyayyen Naimat na ainahi , Don ya gabatar masu da Ibrahim a matsayin wanda ke son yar so da aure, Garin can ciki ne irin babakun arnan dajin nan ne wa yanda ko Christianity din basu damu dashi ba sam, Da farko sunyi murna amma daga baya da suka ji cewa ai Ibrahim musulumi ne sai murnan su ya koma cikki Nan da nan suka hau ihu cewa su sam basu yarda ba Don suna da labarin irin irin wa yan nan musulumai din, Sai da kyat aka samu wani dan tsoho daga cikin su ya sa su amince da zancen, Don haka dama shi Yusuf yasan halin mutanen su na daji shi yasa ya shigo garin da shirin shi Kyauntan goro da kudi yai taba manyan su sai addua irin na kafirci ya tashi, Daga karshe sun yardan mai cewa ba komai kamar yadda ya irike ta agurin shi tun farko, Ko yanzu yaci gaba da hakan ba matsala yana iya yai mata aure, Da kwarin gwiwar shi ya dawo inda yazo yaci gaba da karasa abubuwan da,suka rage daga fannin shi, A kwance take saboda yau kusan kwana biyu ke nan tana fama da zazzabi mai sa zafin jiki, Duk yadda Anty taso akai ta asibiti sam maryam taki, Saboda mugun tsoron alluran da take ji, arayuwan ta, Hakan yasa Anty Dije ta kyale ta a gida sai paracetamol take ta din kira mata, Koshi kamar zata amaye duk cikin ta idan ta sha shi, sai saa yake tsaya mata, a ciki, Naimat ce ke ta faman da wainiya da ita inda maryam din sai godiya take zabga mata, Ruwa masu zafi a ka bata ta watsa wanan ne sanadiyar samun yin barci da tayi, Barci mai nauyi yai awon gaba da ita a lokacin saboda irin yadda taji jikin ta yai dan mata kwari, Yau su Assalam suna gida suna wasa koda ya iso da murnan su da ihu a gurguje suka tare shi, Yana murmushi ya rungumay su a jikin shi, Assalam ne ke cewa uncle ba ka zo mun je shan ice cream ba Assalam yace har hawa saman lilo Issalam ce tace ba Uncle din little Mum yakai mu ba ranan da ita, kuma,,,, Wani iri yaji azuciyar shi amma sai ya dake kawai batare da ya nuna wani kaduwa ba, Duk kowa da ya kamata ya gani na gidan ya ganshi sai ita kadai ce bai gani ba, Ya rasa yadda zai tambaya ko ina maryam din take Naimat ce yau ke zirgazirgan kawo mai abinci sabanin maryam din, Da yaren su yace wa Naimat yau ina wanan yariyar ne what are they calling her,? Wani mugun murmushi Naimat ta kumay a cikin cikin ta ,amma a fili sai tace O, wo, Maryam Ai tana daki bata da lafiya kwana biyu ke nan, Da,sauri ya cire cup din ruwan da yakai bakin shi saura kiris ya kware da shi, Cikin damuwa yace may ke damun tane haka ? Fever ne nake gani saboda bata je asibiti ba balle a ji ko may ke damun ta, Lokacin Ànty Dije ta iso gurin da dauke da tiren abinci a hannun ta, Kara gaisawa sukayi inda take tambayar shi lafiyan Abdull Kuma tana mai korafin may yasa bai zo da shi ba a gwada mai na hausa a gani, tunda ance convolution ne ke damun shi, Aikin shi yayi watau murmushi, batare da yace komai ba, akan zancen, Ashe little mum bata da lafiya, ne ? Ya tambayi anty a takaice, Wallahi fa kadai Yusuf kasan halin ciwon ta bata shan magani bata son allura kuma, Cak ya mike yana mai cewa, yana ina ne ? Yau ne rana na farko da ya taba shiga wani daki dake a cikin gidan duk shigowan da yakeyi gidan, Saboda shi mutum ne mai kokarin tsare mutuncin shi baya wuce gona da iri, Tambaya ya yi da cewa tana cikki ne ansa taba shi rai a bace mata, Kai tsaye ya nufi hanyar shiga dakin inda Anty Dije ta daga kai tabi bayan shi da kallo, Tausayi da kuma kaunar irin halaiyar shi na kulawa da na tare da shi , A kofar ya tsaya yana sallama a hankali, jin ba a ansa mai ba yasa shi kutsa kai cikin dakin, Kwance take tana barci a cikin wani blanket brown, mai jikin mussa, A hankali take mai da numfashin ta guda guda, Naimat ce ta biyo shi dakin, Motsin da taji daga cikin barcin shi ya sanya ta bude, idon ta a hankali ta sauke su a cikin idon shi cak, A rau nane ya kira sunan ta a lokacin da take yun kurin tashi zaune, Sai dai ina nauyin jikin ta bai bari ta iya tashi zaune dan, sam bata jin dadi,jikin ta gaba daya a lokacin, A hankali ta furta sannu da zuwa ya Yusuf, cikin daure da nuna jin zafin ciwo a fuskan ta, Duk da a kwance take bai hana shi gane cewa ta ramay ba,sosai tai wani yar fayo da ita, Gab da bakin gadon ya isa yana kallon ta, A hankali yace maryam may ke damun ki ne wai haka ? Kanta takara mayarwa a filo ta re da cewa babu komai, A rau nane yace ki tashi muje asibiti a diba lafiyan ki pls, Banza tayi da shi tankar bata ji shi ba, don in akwai abin da tai hating shi zuwa asibiti, Anty Dije ce tashigo dakin itama a lokacin tun a kofa taji muryan shi yana cewa ta tashi su tafo asibitin Baki ta tabe tace lalai kina da aiki maryam ace kina ciwo babu zuwa koda dan chemist, Kina kwance ba wani maganin kwarai da kike sha,. Kan shi ya dan girgiza yace bari kawai mutafi asibitin ina ga zai fi ai ko yana mai kallon maryam din, Mikewa yayi yanufi kofar fita ya na cewa Naimat ta shirya ta su samay shi a waje,, Batare da jiran jin ansar may zatace ba kawai ya fice da ga dakin, Tsam tayi tai wani narai,nairai da ido kamar wace zatai kuka, Tunda take ba,a taba yi mata irin wanan shi,shigin ba,irin haka, A dadafe suka fito da ita, da Naimat, daga cikin gida, Tsaye yake jingine a jikin motar shi,yana kallon yadda suke tafiya, Wani tsadaden murmushi, ya sakar masu don ganin yadda suke tafiya tankar bata da jini a jiki, Kanta ta kawar gefe cike da jin haushinsa, na yadda ya jagulamata tsari sai ta tafi hospital, Likita ya auna ta yace high fever ne yai mata yawa, Amma za ai mata,allurai da sauran test test, da ya kamata ayi, Aiko gurin allura akai ta fama da Maryam, din sai da kyat da boni aka samu akai mata, Sun sha dariya sosai shi da Naimat don har kuka sai da tayi gurin yin alluran, A falon suka samu Anty Dije zaune nan suka zube har maryam din wace ke dan dukunkune cikin hijab din ta, Sannu anty taiwa maryam tana sheda masu cewa ko zata sha tea ne, Kai kawai Maryam ta girgiza alamar a,a bazata sha ba, Yusuf yace a hado tea din a kawo mai zai bata da kan shi, Kujerar da take a zaune ya zauna a mafi kusa dashi, Cup din tea din yadago daniyar kai mata a bakin ta, Da sauri ta kauda kaj tace a hankali cikin muryan irin ta mai jin jiki, Zan sha da kai na pls Ido ya kafe ta dashi inda babu shiri ta fara kurba a hankali tana dan lumshe idon ta, Sai da tayi rabin kofin tukun sanan a hankali tace ta koshi, Wani yaro ne yashi a lokacin yana cewa wai a fadawa maryam A, A yana magana da ita awaje,, Gaba daya gurin yai tsit inda Naimat ce tace kaje kace bata da lafiya kaji, Bayan kujerar ta koma ta kwanta kawai ta na mai , maida numfashi guda guda, Yaron ne yadawo yana cewa wai yace yasani gaishe tane yazo yi, dama, Amma wai ga wanan akawo mata leda ne shake da kayan fruit, A gaban Yusuf wanda ko kallon arziki yaron bai ishe ta ba, Batare da yadaga kai ba yace wa yaron kai zo nan dauki ledan ka kai gidan ku kace arabawa kan,nin ka kaji, Basu Maryam da Naimat ba har Anty Dije saida hankalin ta ya dan tu humi Yusuf, din Wanan fruit, din daine bai min ba a zuciya na bari zan samo maku masu kyau, Wani ajiyan zuciya yayi gami da fesar da wata iska mai sauke relief, Gyara zaman shi yayi wani irin mugun haushi ne yake ji a zuciyar shi, Baban su Anty Dije ce yazo gidan don gaida maryan da jiki Tunda Anty Dije tace mai ai maryam bata da lafiya har sosai, Baba ya tausayawa maryama yadda yaga ta koma, Anty ce ke fada ma Baba cewa yanzu Yusuf ya kaita asibiti, Juyawa baba yayi inda Yusuf yake zaune yana kokarin hada maganin da maryam din zata sha, Cikin tausar da murya baba yace kai wanan yaron Allah yai maka albarka kaji, Ban san may zan maka in saka ma da alherin da kake muna ba, Kai haba dai baba ai duk yiwa kai ne wanan baba idan ban maka ba wazan mawa irin haka Dakai da iyalen ka kun nuna min kauna da yarda a fili baba bakku taba yi min wani abinda zai nuna min cewa ni badaga cikin zurian ku nake ba,, Anty Dije ce take ce wa baba kako ji yadda akai mai, a gidan yarinyar da yake bida, Ta, ce wallahi baba mugun zagi akan wai iyayen Yusuf ba musulmai ba ne, Nan dai ta kwashe komai ta shedawa baba yadda akayi, Baba sai faman kada kai yake yi don al,ajabin maganar da yaje ji Baba yace wai ina ki ke, Dije ? Ta amsa da cewa naam baba, In har abin ya zama haka ga kaunar shi nan ai sai su shirya ko ? ,,,,, ,,,,,,,, ,,,,,,,,, ,,,,, ,,,,,,,, SEENABU ZEEE IDRIS MAKAWA, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA IYAKA NA ABBUD WA,IYAKKA NA,STA,IN Gyaran muryan da baba yayi ne yadawo da duk kusan wanda ke acikin falon da tunanen shi, A hankali maryam wace ga zafin ciwo ga kuma nauyin maganar baba a tare da Ta dago ganin ta ido taf da hawaye wani na bin wani, Tace cikin kwantar da murya baba may zai sa ai mun wanan acikin yan uwana ? Baba ko don ban da uwa a gidan zai ai mun irin wanan acikin mu, Baba kasan cewa ina da wanda nake so zan aura don may za ai min wanan hadin tankar wace bata da gata, Murmushi baba yayi kafin ya kauda kai ga kallon mamakin da yake yar tashi da yai bugun gaba da ita, Sai baba bai taba tsan manin cewa maryam zata iya yi mai haka ba, Maryam wani irin daci taji a zuciyar ta ya wani tokare mata makoshi Baba kaji tausayi na kada kasani abin da ba ra,ayina ba,,,,,,,, Bata kara sa maganar ba Anty Dije ta daka mata wani irin tsawa a lokacin, Murmushi baba yakara yi yace maryam may yai zafi haka , Ki kwantar da hankalinki ki bi zabin da nai maki zaki ga alheri a cikjn sa Ni mahaifin ki na bazan cutar da ke ba har abada, ke dace zan iya bugun gaba dake a hanlin yanzu ba tare da na samu wani matsala ba,,,,, Kasa karasa maganar yayi saboda ta makale mashi ,, Sai kawai yamike batare da cewa kowa kallah lahu ba ya mike yafita Yusuf wanda ke zaune tun fara zancen kamar ruwa ya cinye shi bai ce kala ba, Ya mike yabi bayan baba, Don yaga ya fita lafiya a irin yadda ya bar gidan a cikin bacin rai, Wajen minti talatin bayan fitan Yusuf da baba, Ba wanda ya kara, magana kowa da abinda yake sakawa azuciyar shi, Jiki babu kwari maryam ta mike tayi cikin dakin su inda tana shiga ta rusa wani irin ihun kuka cikin ban tausayi, Sai da tayi kukanta ta ci mai isar ta batare da kowa ya shigo gurin ta ba, Anty Dije ce ta shigo dakin da sallamar ta gami da tura kofan, Dauke take da kulan abinci da kwayoyin maganin maryam, A kwance maryam din take a takure, guri guda can gefen gadon ta, Maryam takira sunan ta, kamar wace zatai kuka itama don ganin irin yana yin da yar uwar ts ke ciki, Wani irin kuka maryam din takara sawa wanda yasa jikin Anty Dije makyarkyata, Saboda sam bata taba ganin maryam din ta acikin yanayi irin haka ba, Hasalima dai sam ita bataso baba ya yanke irin wanan hukuncin akan yar uwar ta ,taba, Maryam ta kara ambatawa cikin sarkewar murya tana cewa, Zauna tayi a bakin gadon dab da yar kaunar na ya Hannu takai saman jikin maryam din wace jikin ta a hanlin yanzu yai wani irin zafi radau, Ido ta tsura mata sai kuma taji saukan hawaye ita ma a idon nata, Magana ta fara yi kamar haka, Kiyi hakkuri maryam da hukuncin da hukuncin da baba ya zartan batare da yin wata shawara akai ba, A halin yanzu babu abin da zamuyi akai sai dai mu bari har zuwa lokacin da hankalin shi ya kwanta, A hankali maryam ta taso cikin yanayin jin jikin da takeyi ta kwantar da kanta a saman ciyar yar nata, Tace Anty da gaske ko dai baba baya so na ne kamar sauran diyan shi? Da sauri Anty Dije ta toshe mata baki, Hawaye wasu na bin wasu ta, ta ce maryam kada fa don rayuwan ki ya baci, ki kama sake maganar da bai dace ba akai, Yanzu karbi magani ki sha maryam insaha Allah zan san yadda na bullowa baba yafita batun wanan zancen, Anty don Allah kada ki bari a rabani da A,A saboda ina son shi kamar yadda yake so na, Wani irin kululu cikin ta ya yi tace subbahanallahi maryam ai komai na Allah, Murya kasa,kasa tace irin ta may jin jiki tace don Allah anty ki taimaka min kada baba yai min haka pls Anty, Ta kara riko hannun Antyn na ta tarike su gam tana she,shekar kuka, Da kyat Anty maryam ta samu maryam ta dan sha ruwan kunun da takawo mata tare da bata maganin ta don ta sha, Da kyat ta hade maganin da take ji tankar tana hadiyan guba ne a lokacin, Yusuf wanda ke jin kanshi tankar zai tsage mai gida biyu, a lokacin, Tunda yafita waje ya hango baba har ya sha kwanar xuwa gidan shi, ko, Don haka sai yaji sam baya da bukatar komawa cikin gidan, Kawai sai ya sa kai ya shige motar shi kan shi yake ji yana mai wani irin dan ciwo, ciwo kadan kadan Sannu sannu yana jin muryan maryam yadda take wa mahaifin ta kuka Abin na,soya mai zuciyar shi ciwon kan shi ya na karuwa a lokacin, Yana shiga gidan shi yaron gidan shi mai kula da gida yana ganin shi ya taso cikin murna Amma yau sai ya kula da cewa Yusuf maigidan nadhi bai a cikin hankalin shi, Don haka bayan sannun da yai mai sai kawai ya fara kwasan kayan maigidan nashi yana shiga da su ciki, A hankali ya tura kofan falon sanyi da kamshi ne suka daki hancin shi duk da bacin ran da yake ciki bai hana ya jinjina wa yaron mai kula da gidan ba a irin yadda yake kula mai da gida, Saman kujerar falo mai kama da Royal chair ya fada a saman kujera daya, Yana dafe da goshin shi da yake ji yana kokarin tsage mai gida biyu, Hannin shi guda dafe da goshin shi kan shi na dage yana yana kallon sama, Idon shi a rufe suke ga kuma hannun shi dafe da goshin shi, Maganganun da maryam taita jero wa mahaifin ta a gaban idon shi suke mai yawo a cikin kwakwalwa, Baba may zai sa ai mun haka a cikin yan uwa na da kowa ? Baba ko don banda uwa a gidan za aimun irin wanan a gidan, Ritse idon shi yayi maganar na ci mai rai, Baba kasan cewa ina da wanda nake so yake so na, zan aura, Don may za ai mun irin wanan hadin tankar wace bata da gata, Subbahanallah ya furta ya furzar da iska mai zafi daga bakin shi irin iskan da ke sauke relief a lokaci guda, Shi Yusuf mai ke faruwa dashi ne haka da har zai zama abin kyama a lokaci guda, May mutane ke kyama agare shi da har suke gudun shi haka Yau gashi har da mutanen da a yanzu yake jin su tankar wani sashe na cikin jikin shi, A gaban idon shi maryam ta nuna bata kaunar shi sam Duk da dai shima din bawai kaunar ta yakeyi ba, amma ai bai dace tai wanan kalaman a gaban shi ba, Wata zuciya tace, kyamar ka takeyi ita ma ai, Da sauri kuma zuciyar shi ta raya mai da cewa kai yarinya ce shatab, shi ya kawo hakan, Kawai sai yaji wasu hawaye masu dumi suna bin fuskan shi, Yau shi Yusuf dake jin kanshi a cikin dubu akewa gudun asali irin haka, Gam ya ritse idon shi mai yasa mutane ba su da fahintar maganar Allah ne, May aciki don shi yana musulmi yan uwan shi na Christian, Har kan su da ban tashi daban kuma ma ai yana fatan a ce su ma sun musulunta, din Karan da wayar shi tayi ne yasa shi sauri dagowa daga cikin zurfin tunanen da ya shiga, Anty Dije ce ke kiran nashi kamar ya share ta sai yaga rashin kyautawar haka fon dai ita batai mai komai ba ai, Yana dauka batare da ko sallama ba yaji muryan ta tana cewa, Yusuf kana ina ne wai baka shigo ba tun da zu gashi dare nayi, Sai a lokacin da yaji tace hakan ne ya daga ido ya dubi window dakin yaga gari duk ya gauraye da duhu, Zubur ya mike saboda sallah da bai yi ba na magrib da isha,i Cikin yanayin magana wani iri kamar wanda ya dade yana jinya Yace ina gida ai Anty bazan samu zuwa ba zan dan fita unguwa ne yanzu, Ba,wai ta yarda da zancen shi ba ta amsa mai da cewa, ok to Allah ya tsare, Ya ansa da fadar ameen yana mai kashe wayar shi saboda bai son yakara koda wani kalma ne a kai, A dadafe ya isa cikin kuryan dakin shi bai tsaya komai ba yafada bayi don ya gabatar da alwala yai sallah, Sai washegari yasamu shigowa gidan anty don ya karya, Duk da bai ganta ba kawai sai ya tsunci kan shi yau da jin nauyin sukamar may daga Anty har Maryam din, Saboda dai shi yanzu yasan cewa abin tausayi yake, don har da yar karamar yarinya tana kyamar shi, Gaisawa kawai yayi da Anty sai yaji bama zai iya hira da ita ba yau sam irin yadda su ka saba yi, Ita dai Anty Dije tsayin lokaci tana zaune a gefe tana shayar da yaron ta, Babu wanda ya iya cewa kala daga cikin su falon yai shiru, in ka cire karar na,urorin dake aiki a ciki Sai ko ajiyan zuya da,su keyi a jefi jefi, Anty Dije ce ta kau da shirun na yadda taga Yusuf din ya daure fuska yakuna sauya mata yau Tagumi ta dan zuba tana mai kura mai idon ta A gogon dake daure a hannun shi, ta ga ya kalla,sai kuma ya ja wata yar tsuki, Anty Dije ta dan dago kai ta dube shi tace haba Yusuf ban zaci cewa kaima zaka biyewa halin yarinta irin wanda maryam tayi jiya a gaban kowa ba, Murmushin yake ya ka,karo a fuskan shi yace haba Anty ba wanan zancen ke damuna ba Sada kan shi yayi kasa kamar mai tuna nen wani abu mai nauyi, Kan shi ya dago daga kasan da yasada din yana mai kokarin kara kakaro murmushi, Murya kasa kasa ya ce Anty na fahinci kowa na guduna yanzu, Kasan cewa ta acikin al,umman hausawa kuma musulmai, Maryam wace tun shigowar shi gidan idon ta biyu tana sauraren su, Wani irin abune ya soki kirjin ta don jin abinda yace a gamay da kan shi, Da sauri Anty Dije ta tare shi da cewa haba Yusuf ban taba tsan manin jin wanan kalamin daga bakin ka ba, Maryam sam ba nufin ta ke nan ba a,kan ka, ita irin yadda baba yai matane a gaban mutane zai ce wai ya baka ita idan kun shirya, Alhalin kuma yasan cewa tana da wanda take so tun farko a rayuwan ta, Sakin wani murmushin takaici yayi yace, haba Anty akwai fa alamar tambaya a irin yadda maryam ta dinga magana a gaban baba jiyan, Sanin halin ta da kowa yayi cewa yarinya ce mai ladabi ita, Wani irin tausayin shi Anty Dije taji a lokacin da yake wa yan nan maganganun, Da sauri tace Yusuf na fadama cewa ka daina irin wanan tunanen hakan zai saka shiga cikin wani yanayi har ka fada sabon Allah, Baice kala ba again sai ma mikewa da yayi da nufin wucewa alokacin Tambayar shi Anty tayi cikin kulawa kamar yadda yaya takan yiwa dan kanin ta idan ya shiga wani hali, Tafiya zakayi yanzu baka bari har zuwa anjima idan rana yai sanyi, A nutse yace mata gida zan koma in dan kwanta, Sai dai abin da bata sani ba shine cewa daga nan gidan ta Abuja ya wuce direct. Sai zuwa dare da bata ga ya shigo ba tai mai waya yake sheda mata cewa ai gashi ya kusa shiga garin Abuja Sosai ran Anty Dije ya baci sai kawai ma taji bataji dadin wanan zancen da baba yayi ba, Don kada ya tarwatsa masu zumuncin su da suka dade sunayin abin su gwanin ban sha,awa, Tafiyan shi ya yi wa maryam dadi sosai don koba komai zata dan samu enough time na tunane ta dan sake jikin ta, Sati biyu da wannan zance maryam ta dan sake jikin ta yanzu saboda taji ba wanda ya kara zance, Saidai matsalar ta kawai shine baba, don har yanzu bai karba mata gaisuwar ta kamar da, Amma hakan baisa ta damu ba don ta san cewa wata rana zasu shirya ai, A cikin haka Anty Dije ta samu baba da zancen don ganin irin yadda ya dauzafi ga maganar, Baba yace duk wanan abin da kikaga nayi Dije don Allah nayi sai kuma na biyu don ke da shi yaron, Yanzu wa kike ganin zai dauki yar shi yaba shi kai tsaye a irin yadda aka san halin mahaifin shi, Amma idan maryam ta aure shi duk wani mai ganin cewa baida asalin kwarai zai daina hangen hakan, Ko don ita matsayin ta na yar kasa zai sa jama,a da dama kara hurda dashi har addinin,shi yakara karfafa, Ajiyan zuciya Anty Dije tayi don jin irin hikimar da yasa baba yankewa yar kaunata dakuma Yusuf wanan irin matakin, A gaskiya itama zata dauki nata irin matakin gurin, ganin cewa ta yi wani abu akai don karfafa wanan zancen, Yusuf yana Lagos saboda wani aikin da ya tafi yi gurin, depot din su, Don yanzu ya koma harkan business din mai sosai fiye da da, Don an gyara masu gurin matatar man su, da suke business tun farko, Wayan Anty Dije ne ya shigo mai alokacin yana tsaka ga aikin a cikin wasu takardun su, Fuskan shi dauke da yalwataccen fara,a tankar Antyn tana kusa dashi a,lokacin, Nan ya shiga sosai ranan sukayi hira inda yake sheda mata cewa yanzu businesses din shi na Lagos ya tashi sosai zai ci gaba da harkan man petroleum, Tai mashi murna sosai sai daga karshe ne takira sunan shi a cikjn natsuwa, hakan ya tabbatar mai da cewa za tai serious magana dashi ke nan, Anty Dije tace Yusuf may yasa yanzu ka daina duk wani korin irin yadda kake yi gurin sada zumunci da sauran su, Shiru yayi a lokacin da take maganar tankar bai saman layin sai da tace hlo taji ya ansa, sanan ta tabbatar da cewa yana saman layin, Amsa mata yayi da fadi, No, wallahi ba hakana bane, Kawai dai aiyuka ne sukai min yawa amma da zaran na samu chains zan shigo insha Allah, Shigowar su Assalam yaji muryan su ta cikin wayar, Hakan yasa shi cewa abashi yaran su gaisa da su, Sosak sukayi hira da su Assalam din inda yaran suka ce mai ga Anty Naimat da little Mum, Maryam da ke kokarin kwankwatsa waken da za suyi miya a cikin turmi, tai wani irin saurin juyowa cikin watsa masu harara, Ya dade da Naimat suna waya sai daga baya taba maryam din, Wace a lokacin tana bakin famfo tana wanke kayan miya,, A hankali yakira sunan ta yana mai tambayar ta lafiyan jikin ta inda ta ansa mai da cewa da sauki Ya kuma tambaye ta ya karatu ta ansa shima da fadin lafiya lau,,,, Sai kuma shiru ya biyo bayan zancen don baida a bin fada mata kuma,,,, SEENABU ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, IYYA,KA NA,ABBUD WA,IYYAKA, NA,STA,INN BAZAN IYA MAN,TAWA DA KE BA YAR UWA MASOYIYA, (ANTYN NICE,) Wanan wayar da sukayi yakawo karshen nauyi da kunyar da kowan su ke faman dako a cikin zuciyar shi, Da sannu suka dan fara sakewa da junar su kamar yadda suke a da, indan yai waya da kowan su, zai gaisai, Wanan shigowar ba karamin shigowa yusuf yayi ba don yashigo da shirin auren Naimat, Sosai jama,a ke murna da zuwan shi saboda irin yadda mutane ke a cikin matsuwa, Baida wani hutu atare da shi kasan cewar shine uban amarya da ango gaba daya, Gida na musan man ya sai masu inda ya mallakawa Ibrahim shi a kyata, Anty Dije ita ce uwar amarya don itace komai na amarya, Sosai take gyaran amarya irin gyaran mutanen kasar kwantagora na asali bawai na zamani ba, Don ita da kanta tasa a samo mata ganye don yin hadin da kanta, Kamar yadda ko wace amarya yar asali take zama yayin zaman lalai haka itama Naimat ta koma inda tasha wankan lalai da turare sai sheki takeyi, Su maryam da safiya da wata sister din mijin anty sune a matsayin abokan amarya,, Sai zirga zirga sukeyi akan duk wani abin da ya dace suyi, Shigar wasu shadda maryam tayi masu ruwan pink colour, Sai wani farin lece da akai mai ado dashi kamar flower, Farin gyale ne tadan yafa a kan,ta da takalmi farare masu dan tsini a baya, Daga gurin sayen kayan da zasu rabawa friends din su da suka gaiyata suke tare da safiya amma safiya tadan tsaya sayen wasu kayan A gajiye ta shigo falon hankalin ta a kwance tana mai cewa wassshhh wallahi anty nagaji ga mai manshin din da na hau yana ta tsula gudu da,,,,, Makalewa maganar tai mata don ganin Yusuf wanda ke zaune,a falon su biyu zaune shi da Anty Dije Sam bata tsan manci ganin shi ba a folon don motar shi bata gurin balle tagane cewa yana cikin gidan Daganin ya na yin zaman su ,kasan cewa magana sukeyi mai muhinman ci , A tsakanin su don Naimat ma bata gurin alokacin, Tun bayan wancan rikicin, sai yau sukayi ido biyu da junar su shi, da ita, Kamar ta juya baya ta koma amma sai ta daure, kawai tasa kai ta shiga, A sanyaye ta yi sallama ta shigo falon idanun ta sunyi, wani lub da su saboda kwaliyar da tayi, Fuskanta babu yabo babu fallasa, ta,gaishe su a cikin girmamawa, Yusuf ne ke cewa daga ina take haka take cewa ana gudu da ita a mashin, Maryam ba kyaji ko ? Har yanzu baki bar hawan mashin ba ko a dinga wulwulaku a titi, Yakarasa zancen shi a cikin nuna bacin rai Juyawa yayi inda anty take yana mai facing din ta ya ce, Anty ku koyi tukin mota mana pls a , aje maku mota a gida yafi hakan ? Dariya ma maganar shi ya ba Anty a lokacin irin yadda ya hakikance yana faman fada, To Yusuf in banda abinka abinda mutum bai,dashi ai sai ya yi hakkuri, Maryam na jin yadda yake ta faman sababi sai kawai ta juya, zuwa dakin su, Duk sauran zancen da sukeyi a kai maryam wace ke ta ciki tana jin su duk ranta abace, Don dai ko A,A wanda zai aure ta ai ba zai zake yana mata irin wanan masifan ba, Shigowar safiya a dakin ita agajiye yasa ta dan sakewa ta daina kumburin da takeyi, Sosai suka baje kayan da suka sayo don na su irin sha,anin suna dibawa, gaba dayan su har anty, Muryan Anty ce maryam taji tana kiran ta bayan sun gama kallon kayan da arranging din komai, Da sauri maryam din tace naam Anty, Bata kara cewa komai ba sai kuma tai shiru tana mai kurawa kaunar naya ido, Kamar mai tunanen wani abu can sai tace, wa maryam din, May yasa dazun Yusuf yana maki fadan hawa mashin kika wuce ki ka barshi batare da kin tsaya ba, Wani irin tsoro ne ya lullube maryam din don jin an anbaci sunan Yusuf wai kuma tai mashi laifi, A hankali maryam ta janye hannunta asaman wani kwalin sweet da tadora akai, Kanta ta dukar kasa tana dan wasa da yatsun ta a saman ties, Karo na biyu takara kiran su nan ta tace, kina jina kuwa, Maryam sam bana son ki nunawa Yusuf wani mugun tsana wanda har zai zaci ko kyamar,shi kike ji kamar yadda yake zato, Dan juyawa Anty ta yi inda Safiya take tana mai,cewa don Allah dai safiya idan mutum, Ya nuna cewa ya damu da kai a matsayin dan uwa ko kuma wani nashi can,? May ya kamata kai kayi mashi a lokacin, Safiya tace kai ma kabashi kulawa mana fiye da yadda ya nuna ma, Masha Allah, inji Anty amma ita kinga sam bata gane hakan ba a rayuwar ta, Kin gani yadda ki kayi dazun sam wallahi bai yi daidai ba Hakan zai iya fusata shi yadauki zancen da baba yayi akan ku bilhakki da gaskiya, Kin ko san cewa baba zai iya yin komai ba tare da amincewar ki ba, Tagumi maryam tayi tana sauraron Antyn nata acikin natsuwa, Inda Anty da safiya sukaci gaba da kawo mata musalai kala,kala akan zama da mutane A sake murya a raunane tace yanzu yaya zanyi anty in kaucewa gudun magana, ? Abinda anty ke son ji ke nan dama sai tadan gyara zaman ta tace, Ki nuna mai cewa ke yanzu baki da dan uwan da ya wuce shi, Shawaran ki, ki dinga sanar da shi don jin ra,ayin shi Kissa dai irin ta mata zaki dinga gwada mai tankar ba komai a tare da zuciyar ki, Kinga koda baba zai kara waiwayan zance shi Yusuf din da kanshi zai nuna wa baba rashin dacewar hakan a tsakanin ku, Cikin sauri maryam ta daga kai takalli anty dije tace, Amma anty baki ganin idan baba yaga haka zai zaci cewa ko na yarda ne, Murmushi anty dije takarayi tace, ai shi Yusuf din sam bazai yarda har hakan yafaru ba, Ke wayo fa za muimasu shi da baba din , ke dai iyaka kiyi kokarin nuna mai cewa ba komai na jin kyama a tsakanin ku, A sanyaye maryam tai ajiyan zuciya tace nagode anty, Wallahi har naji wani sanyi a zuciya ta Anan sukaci gaba da hiran duniya saiko ga Naimat wace ta shiga family house din su mijin Anty ta shigo gida, Duk hiran da sukeyi ita maryam hankalinta na can tana tunanen yadda zata fara bullowa Yusuf din,,, Zaune take saman kujera mai zaman mutun biyu, Hannunta rike da waya tana cewa safiya tazo mata da, wani mango drink datake yawan son sha, Safiyan na cewa ita bazata koma baya ba tunda ta wuto gurin ko, Tsuki taja tana cewa macuyiya don kawai kimin keta kin san ban shan duk irin da kika,sayo zaki ce bazaki sayo min ba, Muryan shi taji daidai saitin bayan ta yana cewa kedawa ke fada haka maryam ? Da sauri ta juya bayanta cikin dan tsorata don sam batasan ya shigo gidan ba a lokacin, Bayan ta ta juya sai ta gan shi tsaye cikin wasu kaya masu shigen na indiyan musulmai, Maganar su Anty Dije ne yafado mata arai cikin dan kankanin lokaci Sai cewa tayi cikin dan wani murya kamar mai shagwaba, Wallahi yaya safiya ce muguwa Anty ta aiketa sayen drink shine nace mata, tasayo min irin wanda nake so Amma wai sai ce min tayi wai ita ai ta riga tabar shagon sayarwa ko kuma bazata koma ba, A hankalo ya isa gurin dayan kujerar dake facin din wanda take zaune akai, Cikin mamakin yadda yau ta sake jiki tana mai magana cikin mutunci da nuna kulawa, A dan matse fuska yace ina Assalam da Issi suzo mutafi in kai ku ku sayo, Wani iri maryam taji a cikin ranta na yadda zasu fita a tare gudun kada wani ya gan su ya zaci wani abu, Amma sai gargadin Anty Dije da Safiya ya fado mata a rai, Murmushi tayi a fili tace uncle kada na wahal da kai da abarshi kawai zai fi, Kallo mai kamar harara yai mata yace ku sa may ni a mota pls Kanta kawai ta gyada alamar to, English wear ke ta cikin jikin ta don haka sai ta dauko wani katon hijab din ta , ta feshe shi tsab da kamshi ta zumbuda saman kayan nata, Da ita da yaran suka fita bayan ta shedawa anty inda zasu da uncle din, A can dan nisa kadan da kofar gidan ya parker motar shi, Wata bakar Jeep ce mai kama da wani siffan abin ruwa, Da karasowan su ya bude motar ta yadda zasu shiga ciki dukkan su, Assalam wanda yasaba idan zasu fita ya shige gaba tare da shi Yanzun ma kokarin shiga gaban motar yaron kayi Amma sai Yusuf din yake ce mai, ya koma baya tare da Issi su zauna yabarwa little Mum gaba, Suna barin gurin anty dije wace ke tsaye bayan labule tana leken su tai wani yar ajiyar zuciya, Kira,an shek Ahmad suleman kano ke tashi a cikjn motar a cikin surar Al,imran , Maryam din wace itama bin karatun takeyi a hankali, Inda Yusuf din ke ta sharara gudu a saman titin, Cikin yan mintina kadan sai gasu a bakin wani store wanda akai wa rubutu da manyan haruffa 212 plaza, Shagon yakai shago a wurin girma don haka suna tsayawa a wanan store din, Maryam ta daga kai tun shigowar su motar,ta kalle shi, Yagane may take nufi don haka yadan juya inda su Assalam suke ya ce, Mufita mu zagaya kowa ya dauki abinda yake so kunji, Cikkn zumudi suka firfito zuwa cikkn shagon inda yake rike da hannayen yaran, Itama maryam din dole tabi bayan su badon ranta yaso ba, Sosai suke ta sayayyan su shi da yaran inda yake biye wa duk wani shirmay nasu yana taya su jidan kayan da suke so, agurin, A, baya baya maryam ke bin su wace har zuwa yanzu ko tsinke bata dauka ba, Ganim bata da niyar zuwa yin abinda ya kawo su yasa shi ce mata, Kinfasa sayen drinks din ne ko ? Kai ta gyada mai alamar ,a,a don haka atare gaba dayan su suka tafi gurin,fani abin shaye shaye da yan tonde, tonde, Sai kuma ya wuce zuwa gurin su man gyaran gashi da kayan kamshi dana wanka, Juyowa yayi inda take yace sun ishe, ki ko a kara wasu, Da sauri maryam ta kada kai alamar sun isheta, Gurin biyan kudaden kayan da suka lodo ya nufa inda yabiya su makudan kudi a ka kai masu har cikin motar su, Wanan karon a hankali yake tafiya ba kamar lokacin da zasu zo ba, Sai can daga bisani ya dan karkato kanshi inda take yace, Maryam ina saurayin ki naga tun da nazo ban gan shi yazo ba, Kamar maganar bai soke ta ba tace, kai yaya Yusuf, har da yar kaunar taka kakesawa ido, Surukin kane fa , yaya yusuf takare zancen a cikin zolaya, Tsaki ya ja yana mai yar hararan ta yace, Allah dai ya kiyaye ni surikina mai mutunci ne, Duk da ansar ya bata mata rai amma sai ta cije tace mai cikin dan sasauta murya, Kai ya Yusuf duk wanan biyayya da girmamawan da yake maka, zakace mai hakan ? Tsuki yaja cikin dan sasauta murya, yace, to be Frank maryam wanan guy din wallahi bai dace dake ba sam, Gaban tane ya fafi dammm saboda jin abin da yace, Muryan yaran dake bayane suna kokarin bude wani kwalin biscuit sai fada ga kaure a tsakanin su, Sosai yanzu ya lula a saman titin cikin yan mintina ya iso kofar gidan nasu Tun daga nesa kafin su karasa kofan gidan maryam ta hango motar A,A a tsaye amma yana acikk zaune, Gab da motar shi uncle ya tsaya da tashi motar a gefe guda, Cikin kidimaywa da nuna tsoro maryam ta bakina rawa take cewa malam tun yaushe kazo, shine baka kirani ba, Hararanta yayi cikin daure fuska yace daga motar wa kike maryam, A lokacin Yusuf dake kokarin kwasan kayan da suka,sayo yana jin su, Dukar da kan ta tayi kasa tai shiru, sai daya kara dan dago fuskan shi acikin bacin rai yace, Maryam ban fa fahince ki ba tambayar ki nakeyi fa, Cikin gagawa yake azaman bude kofar motar shi, Ya nunata da yatsan shi yace kada ki raina min wayo ki mai da i ban san abinda nakeyi ba fa pls Nan da nan idon shi ya canza yai wani jajajir tsatsan bacin rai duk ya baiyana a fuskan shi, Sosai rayuwan ta yai mata daci akan irin yadda yake mata agaban mutane, Idanu a runtse tana jin wani irin zafi da bacin rai tace, Dakata malam kadaina fada min irin wanan kalaman,kamar wata yar cikin ka,,, Cike da mamaki A,A ya ware ido yake kallon ta don ta bashi mamaki irin yadda tarufe ido tana bashi ansa, Juyawa tayi kawai zuwa cikin gida batare da takara koda second a gurin ba,,,,, SEENABU MAKAWA,, H🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA IYAKA, NA,ABBUDU WA,IYAKKA NAS,TA INN,,, Har kulun addu,a na,gare ku da fatan alheri ga duk masoya novel din furen juji, Allah yasa a gama da duniya lafiya Allah,sa mu, dace da rahaman Ubangijin mu,,,, 👏👏👏👏👏👏👏👏 Shigowar Maryam ya yi dai dai da fitan Yusuf da ga cikin gidan, Dan gefe ta samu ta dan bashi hanya, tankar baisan cewa da ita a gurin ba ya sa kai zuwa waje abinshi batare da ya ko kalle ta ba, Duk da rayuwan Maryam bai mata dadi ba soboda irn yadda ya nuna mata, A kofar, gida Yusuf ya hango motar Yusuf din yana kokarin barin unguwar, Sau,guda yadan kalli gefen da ya hango motar A ,A din yai wani saurin kauda kan shi, batare tankar A,A yasan da shi a gurin, Sai bayan yaga shigewar shi daga kwanar Yai wani irin dogon tsuki kamar wanda ya ga wani abin ki, ko tsana, A hankali Maryam, takarasa shiga cikin gidan nasu inda ta,samu Anty Dije wace, ke zaune da yaranta duk sun zagaye ta,suna son a bude ledar da sweet din su ke a ciki don su sha, Jiki kamar mai jin kasala ta zube a saman wani kujera da gefen wanda yar ta ke zaune a kai Anty Dije ta dogo kai a hankali ta kalle ta nan take ta fahinci kaunar nata na a cikin yanayi, Gaban ta ya ba da sautin faduwar gaba tana tunanen indai ba wani abin bane ya hada maryam din da Yusuf din ta, Amma to ai shi Yusuf lafiya ya bar su yan inda ma yake sheda masu tana waje tukun, Sai kawai tai saurin kawar da wanan zarkin da zuciyar ta ke kokarin fada mata, Ledojin da yaran ke ta kokarin son ta bude tace wa Assalam ya kwasa ya kai wa maryam, Muryan Sadiya,ce ta suka ji a bayan su tana cewa "Eh" an dawo bari muga abinda aka siyo ma, manyan mata, Sai a lokacin maryam ta maka mata wata hararn "mind you, a cikin wasa, Sadiya din ce takaraso gurin itace ta karbi ledan tafara budewa, Kayan da ta gani fam a ciki da kuma Price's din su ya sa tai saurin dago kai ta kalli inda maryam take zaune, Maryam wacce hankalin ta,bai gurin a lokacin tana kokarin diban wayar da taji sako ya shigo, Muryan sadiya ce, dake kokarin cewa maryam ki ce barna kikayo wa Bros yau, Sai a lokacin idon maryam ya kai a kayan da Sadiya ta zazzage a saman ties kasa, Ba karamin kaduwa tayi ba don ganin irin yawan kayan da Sadiya ta ware cewa, duk nata ne, Baki ta bude da niyar za tai magana sai kuma maganar ta makale mata yakasa fitowa, Guda guda ta dinga bin kayan da kallon har idon ta ya sauka asaman wani dan kit, mai adon ruwan silver, Rashin sani ko may ye a cikin wanan kwalin yasa ta tambaya Sadiya da cewa may ye a cikin kwalin, A hankali sadiya ta bude kwalin wasu set din turare ne kusan kala hudu a ciki, amma duk na desame product, Sai su man shafi masu kyauda da,tsada, kafin su karasa kallo yara suka dinga shigowa da caton din drinks din da ya sayo masu, a can,a Ba Maryam ba har anty da safiya sai da sukai mamaki irin yawan drinks din da a ka shigo da shi, Maryam mamakin ta shine cewa yaushe a har ya sai masu shi bata sani ba, Dai lakacin da suka shiga shagon ya umurci wani da ya loda mashi su a mota, kafin su fito, Safiya ce ta dan juya gefen da maryam take tana cewa, o ya sai ki zo ki ta sha tunda don ki a ka siyo , Batare da maryam tai magana ba tamike kawai niyar wuce wa dakin Muryan Anty Dije ce ke cewa maryam din wa zaki bar wa wanan kayan a,nan, Cak ta tsaya guri guda don jin maganar da yar na ta , ta yi, Idon ta, takai kasa gurin da kayan suke zube, Safiya ce tagani tana ko,karin maida kayan a cikin ledan su, Dukawa tayi ta dauki leda, daya daga cikin ledojin tai gaba kawai a,binta, ta bar sauran inda suke, Bayan ta anty dije tabi da kallo tana mai tausayawa rayuwan yar kaunar nata, Saman kujeran su ta zobe kayan gefen Naimat kadan, Safiya ta biyo bayan ta dauke da sauran kayan a hannun ta, Dai dai, gefen maryam ta zauna inda ta dauki hannun ta ta dora a saman ciyan maryam wace, ke kokarin cire, dan kunnen ta, Sunan maryam din takira a hankali, tare da kara dafa ta don su fuskan ci junar su, Maryam ina son ki bani aron hankalin ki nan ,a cikin murya mai nu fushi maryam din tace ina jinki ai, Murmushi safiya din ta dan yi wanda bai kai ciki ba mai alamar yake, Maryam may ke tsakanin ki da uncle Yusuf, ne ? Batare da ta kalli inda safiya take zaune ba,tace a takaice, may ki ka gani halan, ? Hmmm kawai safiya ta ce ma maryam din don jin ansan da ta bata, a takaice din, Maryam look duk da nasan cewa ,ba wai zaki fada, min ai,nihin gaskiyar zancen gaskiya ba, Akan abin da ke a tsakanin ki da uncle din ba amma aini kuma bawai yarinya ba ce da ba zan iya gane ko may kuke a ciki ba, Kin dai sani, ? Ta karashe zance tana mai yiwa maryam din wani irin mugun kallo , Barin fada maki gaskiya idan zakiyiwa kan ki fada wallah maryam kiwa kan ki don naga wankin hula na shirin kai ki dare, Safiya may kike shirin fada min ne wai akan uncle ne ? May ke a tsakanin na dashi ban da mutuci kawai, Amma zaki zo ki wani dinga min tambaya kamar wani ya aiko ki yi min shi, Sanin halin maryam da safiya tayi kawai sai tai dariya maimakon ta mai da zance wasa, Ba kamar yadda ita,maryam din ta dauki maganar tankar da zafi ba, Hakan da maryam din tayi bai hana Safiya ci gaba da mata zancen Yusuf din ba, Maryam kiwa kanki fada wallahi don dai uncle zai so ki ya kuma rike amana, ba kamar yadda A, A da ki,kewa rawan kafa yake gwadamaki ba,, A hasale maryam ta juyo tace kamar may ki ke nufi A,A yake gwada min safiya,? Maryam inji safiya wace ta kira maryam din cikin nuna kulawa, Ki yarda da zance na pls akan cewa da nai maki cewa akwai wani abu a tsakanin ki da uncle yusuf wallahi, Wani irin mugun takaicin safiya ne ya rufewa maryam din ido wanda har yakai ta iya wa safiya din maganar komai a lokacin, A hasale ta juyo da karfi tace Safiya tun,da har kin matsa da,cewa akwai, To kwai din samay don naga cewa magana kawai ki ke son yi, Maimakon safiya din ta biye mata sai ta mike cikin wasa take wa maryam din idan yai tsami ai maji, Don Ruwa Baya Tsami banza inji, Maman Farida,,,,, Sosai suke ta harkokin shirin bukin auren Naimat wanda yanzu saura yan kwanaki kadan ayi shi, Ànty Dije wace tai matukar kokarin wajen ganin cewa taiwa amarya duk wani abin da ya dace ai mata, alokacin aure, Kaya masu kyau nagani na fada yaiwa Naimat din na daki, Sai a,wanan lokacin ne su Anty suka san cewa akwai yan tsirarrun Christiatorchi da dama agari wa yanda suka musulunta, Kamar hadin baki sunyo gaiyyan junar su zuwa gurin karar wanan bukin Maryam wace ke ta kokarin kawo masu ruwan sha tare da abin sha a lokacin tana jin irin yadda suke tawa Naimat murna da arzikin shigowa, cikkn muzulunci, Anan take jin wata far addatijowa tana Naimat magana a cikin gwari gwarin hausan su, Cewa kada kiyar da ki irin musuluntar Nao,mi, wace kusan sau uku tana musulunta tana kuma komawa Christian, Saboda kawai wai ta kashe auren da tayi da musulmi, Wanan maganar da maryam taji a lokacin yai matukar bata mamaki Bata san lokacin da tasa bakin ta azancen ba tana mai tambayar su ko lafiya, ta dinga wanan irin Riddah hakan ? Daya daga cikin matan wata mai hausan da ba daidai ba ta juya gurin da maryam take rike da kwalin drinks a hannun ta tace, acikin magana a hankali da kuma bacin rai da kaico a fuskan ta, Kin san wasu basu da karfin imani a tare da,su, don haka auren da taiwa musulmi da zaran ya mutu sai ta koma matsayin ta na Christian, Idan kuma wani musulmin yazo again ya aure ta sai ta kara canzawa zuwa cikin islama, A haka har tai wanan kusan kashi uku yanzu haka tana a cikin Christian ne, Maryam kara tambayar matar tayi da cewa kuma an kasa samu musulumi wanda zai rike ta, A matsayin amna tun da tana da ra,ayin yin addinin muduluncin, Sai matar tai wani irin daga hannun ta zuwa harba ta rike a cikin nuna wa? Tace wasu maryam wacce tsayuwar ta da zancen da sukeyi ya jawo ra,ayin mutane da dama gurin su, Matar tace ai kin san halin mutanen musulmai yanzu ba wai taimako da sukewa irin wanda ya musulunta haka, San,nan kuma ita wanan matar, kishiyoyin ne ke hana ta zama a gidan mijin, Bawai itace bata son zaman auren ba, saidai kuma mai maimakon idan tafito tasamu gidan wasu musulmai ta zauma a a sai dai kawai ta koma gidan su ta zauna A haka yau da gobe sai kawai muji cewa ai ta koma Christian again, Sai da maryam tai wani irin ajiyar zuciya mai nauyi sai ta ce Allah ya kyauta, Duk gurin suka amsa da fadar Ameen Ameen, gaba daya a lokaci guda, Daga haka maryam ta wuce zuwa gurin da suke aiki sai dai zuciyar ta cushe da bakin cikin halin da wanan matar take ciki, Tun zuwa lokacin da takoma haka kawai sai ta tsinci kanta a cikin damuwa da maganar, To sai dai kuma ta ina zata fara wa zance daga karshe ma zuciyar ta ya bata shawara akan Ita wace,ce da may ma zata iya tallafa mata tai tsuki tana mai cewa ina ma a ce musulman mu masu zuciya ne kamar yan mabiya addinin Christian, Da wanan tunanen suka risketa a zaune, duk sallama da maganar da Jibrin kewa maryam hankalin ta ya zurfafa a cikin tunanen wanan matar da taji labarin ta dazun, Gaba dayan su mamaki yadda yar karamar yarinya take irin wanan zurfafan tunanen da kurciyar ta, Jibrin ne yasa keys din motar shi kusan fuskan ta ya dan kada mata shi a fuska, Firgigit tadawo a cikin hankalin ta yayin da ta sauke idon ta a kan su su uku, Suna tsaye suna mata wani irin kallon mamaki cikin sauri ta dukar da kanta kasa tana mai gaishe su da shigowa a lokacin, Kara tambayar ta Jibrin din yayi a cikin tsigar wasa, Ko dai A, A din ta dan masuga take tunane ya kira mata shi, Murmushi mai kama da harara tai mai tana cewa ai ba sai kakira min shi ba, An fada ma, ni banda wayan kiran shi ne a guri na, Ke dai gaskiya barin kira maki shi kawai, Wani wawan tsuki Yusuf yaja daga bayan Jibrin din yace Ke Maryam Anty tace zaki fitar muna da kulolin abinci ko ? Sai a lokacin maryam ta farga da su a tsaye bayan jibrin Yusuf din wanda tun fara wasan ba,an su yake faman dan,nan wayar shi, kawai, Irin yadda yai magana ta mayar mai da ansa ita ma, Ta mike suka shiga fito masu da yawan kololin abincin da a ka dafa masu don jama,an su, Gaskiya duk sun yaba da irin kalar girkn da anty dije ta tayi ita da sisters din nata, Maryam ce ta dangware wasu set din plates masu yawa a gaban kololin, Yusuf wanda ke can daga bayan su don yaki karaso kusa yadaga wayan shi yana kira, A daidai lokacin da wata daga cikin matan tazo tana mai wani kirari a cikin harshen yaren su, Sai wata yar boyayyar murmushi yake yi a hankali tankar wanda bai son asan may take cewa, Matar ta juya da harshe hausan wanda ke da,surkin yare aciki tana mai cewa wasu jibrin, Wanan da kuna ganin shi a nan, Shan gerin mu shune manya, manya sosai don de baba nashi bai jauna a gida bane Da yan junan yazama serki a gerin na su ko, Kudi masu yawa yafito dasu ya mika mata sai ga sauran matan dake saye da zanin su na IBO Anyi fanti, fatin sama da kasa sai farar bluewers, da gwagwaro a kai, Nan suka shiga raira mai wani waka acikin yaren su suna mai yi mai kirari, Tsatsaye su maryam sukayi suna mai kallon su gwanin ban sha,a wa, KB da Jibrin su ma suka basu kyautan kudi masu yawan gaske, Safiya ce ta dan muntsili maryam din tana mai mata nuni da Yusuf din, Wani irin wawan duka takai ma Safiya din wace ta kauce tana dariya keta, Caraf sai a idon Yusuf wanda, idon shi yakai gare su tun fara wasan nasu, Daure fuskan shi yayi yana mai masu wani kallon ku daina haka man, Duk kan su, suka sun,kuyar da kan su a cikin lokaci guda,cikin jin kunya, Still, uncle inji Safiya ka bari mu ji kirarin ka mana ko zamu iya muma muyi ma, irin shi, Duk daure fuskan shi da yayi sai da maganar safiya ta sa shi yin yar murmushin, Ya dan kada kai yace kai,safiya baki da dama fa, Dariya ta saka mai tana mai jawo maryam, wai zasuyi wa Yusuf din kirari, Kanta ta koma sadawa kasa saboda irin kallon da Yusuf ke mata, Mayar da hankalin shi gurin da kololin abincin suke ya yi Juyawa kawai maryam tayi zuwa dakin, abin ta batare da takara wani abin ba agurin, Ko da ya juyo bai ganta a gurin ba ta wutsiyar idon shi, ya dan hango ta, zata shige daki, Daga cikin daki taji dirin motocin su, sun kwashi kayan abincin zuwa gurin da za ai recipetion, Wanka maryam tayi bayan shigan ta daki inda ta fito cikin wani Dakkaken dinkin shadda din da yusuf ai,kowa Sadiyar, ce daka karshe kuma yace abar ma,maryam din,,, Sune Anty Dije ta bayar akai mata wanan dinkin mai wani hannu shara,shara, Sai lece, da aka darza mai bayan anyi mai aikin wuta, da kuma stone a jikin shi, Kayan light green, sunyi mugun karban jikin ta takai wani lokaci a gaban miro tana gyara jikin ta tsab, Itama dai safiya irin shaddan ta sa sai dai gurin dinki ne kawai suka sha banban dana maryam, Sun kai wani lokaci a cikin daki suna yar hiran su ,saidai muryan mutane da suke ji sama sama a,waje, Da sauri ta mike zuwa waje don tunawa da tayi cewa Anty fa bata gida suna gurin gyarawa Naimat gidan da zasu zauna, Zaune yake shi kadai a cikin falon su, ya dan zauna rigingine. Ya dafe kai da hannu shi guda idon shi a rufe ya lumshe su, Ganin da tai mai haka yasa ta kudirawa barci yake yi a hankan, Juyawa tayi da niyar ta koma cikin daki inda suke ta zabga hiran su, Maryam, yace cikin wata irin nishadaddiyar murya, Cak ta tsaya don jin mai zaice, mata, Still bai kalle ta ba hannun shi ya na dafe da kan shi, Jikin ta taji yai sanyi don irin yadda yai mata, Kan ka ke ciwo ne yaya ta samu kanta da tambayar shi, Shiru nadan lokaci tukun kafin ya cire hannun shi yadan kalle ta da idon shi da su ka kada mai sukai jajir kamar yaci kuka, A hankali ya ce mata may kika gani ne haka ? Cikin dakewa tace idon ka sunyi ja da yawa uncle, Kan sa ya girgiza mata, yace babu wani ciwon kai dake damu na maryam, Illa magana da ke kokarin tarwatsa min zuciya ta, Maryam bana son in na fadawa mutum gaskiya,yana dauka ta tankar banda daraja agurin mutum, Baki ta dan murgada mai kadan tace nidai ya Yusuf na dai kusa aure in huta da duk wanan sa idon da kuke min, Don dai ni banga abin da nake yi ba har kake cewa hakan, Niyar barin gurin tayi tana kun,ku ni, tana cewa wallahi shi yasa bana son shigowar ku KG sam, saboda takura da sa ido, Tajuya kawai abinta, Saidai batai nisa ba ta jiyo muryan shi yana cewa, To aiko nai maki murna da kika fada min cewa, kina son aure kwanan nan Don haka zan je in samu baba da Anty in sheda masu, abinda ki ka ce,, Da sauri ta juyo tana fuskan tar shi batare da wani jin dariri ba ko kunyan shi, Sai dai, kuma wanan karon kamar bashi ke kwance da zu ba, Yanzu a zaune ya kyam,kamar ba shi ba, ya na mata wani kallon cikin zaki gane kuren ki, Ba kunya ta, kama yar hararan shi, tace, ban san may yasa kake yawan samin ido yanzu ba wallahi, Kawai ta juya ta shige abin ta zuwa inda ta hango Naimat zaune tare da bakin ta,,, Bayan ta yabi da kallo a daidai lokacin da kiran sadiyar shi ya shigo mai, Tana mai sheda mai cewa ga ta a kofar gidan Ànty tazo mai buki, Tashi yayi daga inda yake yadan leka inda yaga maryam tabi, Tsaye take sina diban waya ita da Naimat da Safiya, Ganin shi ya leko daga kofan falon yasa su mai da hankali gurin shi banda maryam wace kanta yake duke tana kallon waya, Sunan ta yakira yace tafita waje ta shigo mai da baki pls, Lokacin da ta fita, ta samu su Sadiya ne bakin da yake nufi tai bakin ciki sosai don ita tana ganin cewa yai mata rashin mutunci sosai, Ita Sadiya din bata san kofar shiga gidan bane da zai tura ta taron su, Kallo guda Sadiya tai wa Maryam sai taji wani irin tsanar yarinyar ya kara shiganta, Ita dai sam bata ra,ayin wanan yarinyar a rayuwar ta bata san mo may ya sa ba, Rai a dan bace maryam ta dan tare su inda tai masu iso zuwa cikin gidan, A falo kamar yadda tabar shi su ka samay shi a zaune hankalin shi kwance,,,, SEENABU ZEEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣6⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, IYAKA, NA,ABBUDU WA,IYAKKA, NAS,TA,INN,,, Ina mai baku hakkurin rashin jina da bakuyi ba kwana biyu, da fatan zakuyi hakkuri dani dan Allah, Sanya suke cikin dogayen rigunar shadda mai ruwan powder, wanda dinkin shi ya,kai har kasa kamar yana jan kasa, Hannun dinkin shara,shara, dashi har ya dan zarta hannun su, Takalman su masu tsinin duduge, da su da kuma tsawo, Sai chewing gun dake a bakin su suna taunawa kas,kas, kas, Duk karan chewing gun din ya damu maryam wace ke gaba tana masu jagora zuwa ciki, Idon su kem a kanta, yanayin ta da kuma yanayin shigar ta ya sasu yin hassada da ita a cikin zukatan su, Kayan da ke a jikin ta da nai bayani baya din kin yan Senegal yakarbi jikin ta yai mata dan karen kyau, a jiki, Yana zaune kamar yadda ta bar shi kafin ta fita, Sai dai wanan karon waya ce a hannun shi yake yi, Takon su takalman su da ya cika gidan duk ya ruda ko ina, Wanda hakan ya jawo hankalin mutanen dake ta wajen tsakar gidan zaune, Inda suka zubo masu ido caaaa, suko sai wani ran gwada sukeyi abin su Gurin zama maryam din ta nuna masu saboda samun shi da sukayi yana waya a lokacin, Fita tayi zuwa dauko tire inda ta jero masu abin sha da cups saman ture din, Duk wanda da Yusuf ke yi idon shi sometimes suna gittaiyya akan maryam wace ke sintirin taron baki, A hankali ta dire mazu shi a gaban su inda ya yunkura zuwa dayan kujeran da ke gefen, A lokacin shi ma yusuf din yai sallama da wanda yake waya dashi din, A cikkin wani irin kashe murya Sadiya kewa Yusuf din magana , Ganin haka yasa maryam yunkurin tashi don barin gurin, Shigowan Anty Dije tare da sallama sai yan rakiyan da suka raka ta gurin gyaran gidan suka shigo a gajiye, Yun,kurawa, yayi don ya gyara zaman shi da kyau don gani shigowar su anty gidan, Kallo daya Anty tai masu kawai sai ta wani dan fuske fuskan ta tankar bata ji dadin ganin su ba, Su ma dai ba wai sun sake jiki da ita ba ce a irin yadda su ka gan su, Gaisawa sukayi sama , sama da su anty dije din tankar ba su so ganin ta ba, Yusuf ne ke gaida anty a cikkin kulawa da girmamawa inda yake ta faman yi masu sannu da zuwa, Gaba daya hankalin shi, ya baya gurin da anty dije ke mai bayanin yadda aikin nasu ya kaya, So sai yaji dadin baya nin da Anty Dije ke mai akan irin yadda aikin ya kaya, Sadiya ce cikin wani irin sallon murya ta ce D, Yusuf din wanda ke, magana da Anty yadan juyo gurin ta kadan, Maryam ce tsaye a gefe dauke da ruwan leda tana kokarin rarabawa mutane don su biyar ne suka shigo Cikin wani marairai ce murya take ce mai muna son mu tafi fa, Anty ce tai magana wanan karon da cewa haba ku dan dakata in baku, abin buki pls, Maryam ce tace cikin dan sake fuska tun yanzun nan da shigowar ku har zaku tafi, Sadiya wace tai tankar bata ji ko may maryam din ke fada ba, ta wani share,kawai, Saida ya gaji don kanshi ya mike tsaye yana mai cewa Anty Dije sai an jima idan yadawo, Sai anjima ma da kyat sukewa mutane shi ida suka bi bayan Yusuf din, Su na shiga mota yadan wuce gidan su Anty batare da ya waigo inda Sadiya take zaune ba yace, Sadiya may wanan yarinyar ta tare maki ki ke wani share ta haka, Pls bana son irin haka, Sadiya yace a cikin dakewa, Caraf Sadiya tace Nafa san ko may wanan yarinyar da yar ta muna fuka suke kullawa a kai na, Da wani irin karfi ya faka motar shi wanda har yasa karan motar yajawo hankalin mutane, Ita kan ta sadiyar sai da ta ji tsoron wanan karar amma sai kawai ya dake ya wani matse fuskan shi,ya ce, Kufita min mota, bata motsaba a inda take sai ma ci gaba da taunar chewing gun da tayi, Wani irin tsawa yadaka mata saida ta firgita wanan karon yace ku fita, min nace, Yadda su ka ga fuskan shi ya canza tankar na wani katon zaki yasa su jin tsoron shi, Murya na rawa ka fara cewa, don Allah yayi hakuri ya karasa da su saboda Allah, Sai da yai kamar ya dukar da kan shi saboda yadda yake ji a zuciyar shi, Tankar wani zaki da ya kwana bakwai baici komai ba, Sunan Allah da kawar sadiya ke ta hada su da shi yasa shi tayar da mota ya hau saman titin a hankali, Sai da suka danyi nisa ya sauke wani irin ajiyar zuciya batare da yakalle ta ba yace, Sadiya kinyi babban kuskure na ai,banta Ànty Dije da kikayi a gabana Tun ban aure ki ba kina kokarin rabani da mutanen dake sona da zuciya daya, Mutane da nake jin su tankar yan uwana na ji,ni wa yan da muka fito ciki daya, Matar da itace tasa ni gaba a kan ki wai yau itace kike wa, wanan bakar maganar haka, Cikin rawan murya tace Yusuf don Allah dai kayi hakkuri pls, Yusuf batare da yai magana ba ya kau da kan shi gefe ya na mai fesar da iskan mai huci da zafi, daga bakin shi, Bai karasa kofar gidan su ba ya aje ta tana mai magana ya fisgi motar shi ya bar gurin,,,,,, Kwance take makale da waya a kunen ta daga ita sai wani dan rigar shimi fara mai yar hude, hude, Zani shaddan da ta sa ne daure a jikin ta sai wani dan yalalon gyale da ta rufe fuskan ta da shi, a lokacin, NA,IMAT ce zaune daga gyafe tare da Isslam suna kallo a wayar ta. Ga kuma tv dake cikin falon shima aiki yajeyi a lokacin Sam maryam bataji shigowar Yusuf ba a lokacin saboda hankalin ta da ke gurin wayar tana kokari karkada kafar ta, Kamshin turaren shine ya daki hancin ta ida ta bude idon ta dake a lumshe ta sauke su a cikin idon shi, Saye yake da jallabiya mai ruwan toka, a jikin shi, Sai yar karamar tasbaha da yake dan ja a hannun shi, a hankali, Cikin yare Naimat ta ke gaishe she shi inda ya ansa mta da kada kai alamar ansawa, Muryan maryam yaji tana cewa ai ko ba,a gaiyace, kaba kai nagida ne zaka iya zuwa,, Kanta ta kwantar saman hannun kujerar da take zaune a kai, tana mai ci gaba da wayan ta, Sam ta manta cewa yar shimi ce kawai a jikin ta a lokacin, Kujerar da yake facing din ta ne ya zauna fuska babu walwala, a tare da shi, Fitowar Anty Dije ne daga cikin daki yasa shi dan sake fuska, Sun gaisa take cewa, ya komawar baki dazun da suka shigo,, Sai da ya idar da abinda yake karan tawa ya shafa sanan ya cewa anty dije, Anty wanan yarinyar taban mamaki so sai wallahi, Baidai fada mata ko may ye ba don bazai iya yin magana ba a lokacin irin yadda yake ji a ran shi, Dariya maryam ke yi a lokacin don abin da A,A ya fada mata har tana wani dan kyarkyatawa, Ido ya zuba mata daga inda yake zaune yana mai jefa mata harara, Da sauri maryam ta kauda kan ta daga gare shi don irin yadda yai mata, Kanta na kasa cike da jin nauyin shi don tunawa da tayi cewa,, daga ita sai, yar base a jikin ta, Ta rasa yadda zata mike zuwa cikin dakin su a lokacin, Duk da ya fahinci cewa tana son tashi zuwa ciki sai ya kawar da kan shi gefe tankar bai ganta ba ma agurin, Cikin dabara ta mike zuwa cikin dakin su inda ta karasa yin wayan ta, Har ya gama hiran shi da anty ya bar gidan maryam bata leko wajen falon ba,,,, Bayan ta gama komai tana kokarin kwantawa barci ne taji wayan tana kara, A sanin ta dai sunyi waya dazun sosai da A, A din ta sai kuma dan bankin ta da ya kirata around four na marance, Hannu ta mika ta jawo wayan ta, zuwa fuskanta don ganin kowa ke kiran ta a wanan lokacin, Uncle Yusuf, tagani a rubuce saman screen din wayar nata, Sunan ta kara nanatawa a fili don mamakin da ya mamaye zuciyar ta Da sauri ta dauka don bata san ko may ya sa ya,kirata ba, a daidai wanan lokacin Assalamu Alaikum tace a lokacin da ta dauki wayar, Shima a nashi bangaren wani iri yaji a kunnen shi a lokacin da tai wanan salaman, Shirun da maryam taji yayi ne a lokacin yadan kara sa ta cewa 'Hello" Ajiyan zuciya taji yayi a lokacin inda ta ji shi yana cewa hello, Uncle naga kiran kane shine na dauka, murmushi taji yayi yana mai cewa sorry bake ce ,naje kira ba, Cikin yar muryan nan nata mai kama da sarewa tace ok, Wallahi har gaba na yafadi ina ce ko nai wani laifin ne akakirani ai min fada, Fuskan shi kum she da murmushi ya ce, au ke kuma ba kyason kiyi laifi ko, Tana yar dariya tace to ai kaine uncle ba wai sai mutum yai ma wani lafi ba zaka haushi da fada, Murmushi mai yar sauti ya sake yace ke maryam bana son sheri yaushe nake maki fada ni, A hankali tace ai kai baka sani uncle sai dai kabar mutun yana ji a zuciyar shi, Muryan shi cike da amon dariya yace nagode da wanan kazafin maryam, Lah tace wallahi ba kazafi bane nai ma sai gaskiya kawai, Ni ba ruwana ban ce nai ma kazafi ba ai A hankali yace gaskiya kin min don dai ni na san cewa fada na dake shine a kan hawa mashin ne kawai, Sai kuma taji ya kwantar da muryan shi a hankali yana magana yana cewa, Maganar gaskiya maryam bana son in ga mace wace na sani a kan mashi, wallahi duk nakan ji rai,na ya baci so sai, Balle ke da kike ta daban a guri na maryam don may bazan maki fadar hawan mashin ba, Inda za,a yarda min in saya maki mota batare da an tunhumi komai ba da wallahi na dade da saya maki, Wani irin nauyi da kunya ne ya kamata tankar yana kusa da ita alokacin, Kanta na kasa tana mai kurawa ties din dakin su ido tace , Haba dai uncle kamar wata mai wani matsayi a gurin ka ni a su wa da har za,a sai min mota, Bai yi magana ba amma murmushi yaiwa zancen nata kawai, Ok wait and see yace, mata a hankali, Dariya ta yi mai sauti ta cikin ciki ,kaman ya na mai, ganin, ta,inda take kokari ta shigar da maganar, da cewa ai sai dai Anty Sadiyar ka ko Anty Aisha ko, Sune manyan mata da suka dace da shiga mota a garin nan don a,san suna tare da kai, Duk da ya fahinci irin maganar da tai mai amma sai ya dake da cewa, To sai gashi kuma wace bata kai su ba tana kokarin ta riga su shiga ba, Murya cike da maganar serious yace mata maryam, A gaskiya bana son kina hawan mashin din nan pls, Ya na,nata tambayar shi don jin shirun da yayi ta na bangaren, Yace mata acikin murya mai taushi da Kin ji ? A hankali ta ansa mai da cewa ,"To" uncle, Cikin wata murya yace, mata kin yarda bazaki kara hawa bake nan kin amince, ko ? A hankali takara ansa mai da cewa Eh uncle, Nagode nagode nagode maryam insha Allah zan yi kokarin ganin kin daina kwata,kwata, Kamin wanin su ya kara wani magana, maryam ce tai saurin cewa uncle nagode sai anjima kada na damay ka, Sai ji tayi yace ai idan kece bazan ji damuwa ba maryam Saboda may uncle maryam ta tambaya a kage, Saboda kawai kina kaunata, kina sani natsuwa aduk lokacin da nake waya dake, Baki ta dan tabe, alamar kaji dashi tace ashe kuwa A,A nada gaskiya ako yaushe yake a cikin fushi yace idan ba ya kirani ba baya kan samu relief, A she ko zai daina jin relief idan yai wasa don dai kwanan nan zanwa kaunata aure Don shi naga bada gaskiya yakeyi ba , Dariya maryam tayi wanda bai masan cewa ta iya irin wanan dariyar ba, Tace uncle har ka sani babban dariya ka ma dai yi min miji ke nan ko ? Kanshi ya hirgiza tankar tana ganin shi a gurin yace No but zan dai yi maki soon, Duk a cikin gwarigwarin hausar shi da yar muryan shi mai daukan hankalin mai sauraro suke zan cen, Da haka yana jan ta da hira har dare yadan yi basu ankara ba, Inda duk kan su suka sake suna ta surutu da junar su, Daga karshe maryam ce tace mai ya kwanta hakanan don yasan gobe yana da baki yan daurin aure, Bai musa mata ba sukaui sallama da junar su kowa yana mai farin ciki na rashin sanin dalilin haka, A haka maryam ta kwata da, yar murmushi makale a fuskan ta,,, Washe gari aka daura auren Naimat da Ibrahim akan kudin sadaki naira dubu hamsin Jama,a sun karba gaiyyatar da Yusuf tare da Abdullsamad suka kai masu inda suka sheda wanan daurin auren da akayi, A kofar gidan su Jibbrin wanda mahaifin jibrin din ya zama waliyin amarya Naimat, Bai wani bidia,a ba sai walimar da maza sukayi a kofar garkan gidan Abdulsamad, din, Don haka duk yinin ranan Yusuf bai samu shigowa gidan anty dije ba. Saboda sanin da yayi cewa akwai mata da yawa yan zuwa yinin buki shiko a rayuwar shi baya son yana shiga gurin da taron mata yake,,,, SEENABU ZEE MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR YAURI, Alhamdullahi Rabbil,Alamin Ànty Dije tare da wasu daga cikin yan uwan su ne suka tafi kai amarya gidan ta dake a unguwar GRA, Motoci kusan biyar ne suka zo don daukar a maryan sanin cewa ba wai tana da wasu mutane da yawa bane a garin, So sai ko jama,a suka dan taru don zuwa rakiyar amarya gidan ta, da misalin karfe biyar na marancen, jumma,a, A bin gwanin ban sha,awa saboda irin yadda, mutane sukayi don Anty Dije, kusan duk wace take hurda da ita tazo mata wanan karar na buki, Amarya Naimat tasha ado a cikkn wasu lace farare kal dinkin buba, sai farin mayafi da kuma wani farin sarka mai daukan ido,sai wasu, fararen takalma a kafarta Idon ta alamar taci kuka saboda irin yadda sukayi mata wani irin lub, lub da su, Maryam ce kawai aka bari don tsaron gida tare da kau da sauran kayyayakin amfani da suka bari a waje, Sam bata san shigowar Yusuf din gidan ba saidai muryan shi da ta ji gab da bayan ta, Inda ta juya a yar razane cikin dan rudewa saboda rashin sanin mutum na kusa da ita, Fararen shadda ne a jikin shi dinkin tazar ce har kasa, Hannayen shi a harde saman kafadar shi inda ya kura mata ido kawai a cikin rashin sakin fuska kamar yadda yake a kullun, Sai da tayi kokarin saita kan ta,tukun, na san nan ta samu bakin yi, mai gaisuwa, Ya ansa mata kamar kullun a takaice sai dai na yau yana da dan banbanci da saura, Gurin fridge ya wuce direct inda ya bude ya,dauko goran ruwan Inuwa water, Kafa kai yayi batare da ya jira kofi ba, ya kama kwankwada, inda duk ya kwankwade ruwan tas, Yau she su Anty za su dawo ne maryam wace ke kokarin shiga store din su, dan aje kaya ta ansa mai da cewa, Anjima kadan shiru yayi ba tare da yakara magana ba , Gurin kujera two site ya nufa nan yazube sama yana mai cewa Ya Allah, Akawo ma abinci ne ta tambaye a cikin dan dari, dari, No thanks kawai yace mata inda ya maida idon shi ya kara lumshewa,, Aikin ta taci gaba da yi abin ta batare da takara bi ta kan shi ba, Yusuf wanda ke kwance tankar mai barci sai dai a zahiri idon shi biyu yana tunanen duniya, Wayar shi ce tai kara gurin da, yake aje a gefen shi, A hakali ya mika hannu shi ya dauki wayar sunan Jibrin ya gani, Dan gyara kwanciyar shi,yayi ya na mai kokarin daukar , Tambayar shi Jibrin yake, yi ko yana ina ne haka Sai da ya ja dan guntun tsuki kafni ya ansa mai wayar shi, tu kun, A takaice ya bashi ansa da cewa gidan Anty mana , Jibrin yai yar dariya kafin yai mai magana, tukun Da iskanci ai ba na fadama cewa zan dan gudo in huta ba kafin su dawo, Ansa yabashi da cewa an fa kawo kayan da ya ce akawo mai ga mutumin yana neman shi, Sai da yadan lumshe idon shi, sannan ya dan sukunyar da kan shi yana mai kallon ties din falon yace, Ya ce gaskiya Jibrin bazan iya zuwa in duba ba saboda ina hutawa yanzu, Amma zai iya kuzo nan ai maryam tana gidan sai ta tayaka dubawa, ko, Jibrin din ya ansa mai da cewa gashi nan zuwa tare da mutumin, Yusuf din ya ansa mai da cewa ya yi kyau sai kun ka raso ina ciki idan kunzo, A lokacin ne kuma su Assalam suka shigo gidan daga can cikin gida gurin kakan,nin su, Ganin yana bukatar hutu yasa maryam kiran yaran zuwa gurin datake, Aiko can gurin ta suka dan bata lokaci sai dai jefi,jefi tana kallon shi idon shi a lumshe suke, Ba ai wani dadewa ba Jibrin yai sallama tare da mai kayan, A kofar falo suka yi sallama maryam wace ke zaune da yaran suna kallon a wayar ta takarba masu sallaman su, Dukkan su a falo suka zube sai kayan da mutumin ke kokarin budewa daga cikin wani buhu, Zannuwa masu yawa tagani suna fitar wa daga cikin buhun, Jibrin din ne yasawa maryam wace ke ta waje kira, Sai da ta dan ja aji irin na mata tukun sannan ta mike zuwa ida suke, Tun daga nesa ya tsai da hankalinshi gurin ta irin yadda take tafiya, Tabbas maryam ta, tara abubuwa da dama da sai yanzu yake gani su daga gare ta, Idan ma don kyau ne ta na dashi uwa uba kuma hali duk yarinyar tana da,su, Cikin yaga da nuna isa ta yan matan taka ta iso gare tana mai cewa gata, Tankar ba shine yakare mata wanan kallon ba haka yanzu, Wayar shi kawai yake, ta famar tabawa ya Allah chatin yake yi ko kuma game, Jibrin ne yadan kalle ta yace ki taya mu zaben zani mai kyau daga cikin wa yan nan pls, Kurawa zannuwan ido tayi zuwa dan wani lokaci Sai ta jawo wani mai ruwan zuma, daga ciki yana da wani ado kamar gidan sugar Shi ta mika masu tana mai cewa wanan kamar yafi dama saboda baida ado da yawa so sai, Kai ya daga ya kalle ta da mamaki don jin cewa ra,ayin su yazo daya, da ita, Saboda tun da aka zube zanuwan idon shi yake akan wanda ta zaban Har zata juya don barin gurin saboda rashin sanin ko may za su yi da zannuwa haka, Muryan mutumin taji yana cewa zan,nuwan ai kudin su kaza ne, Dan juyowatayi tace wa mutumin kai malam fadi gaskiya yaushe kudin su ya kai haka, Jibrin yace wa maryam ta fada masu kudin kayan a takaice maryam tafada masu Amma kuma sai tace sai dai in har zasu bashi yadda yace ne saboda tai mako, Dariya duk suka agurin ban da Yusuf wanda dan murmusawa yayi inda ya bukaci mutumin da ya bashi turmi talatin, Yace idan basu isa ba zai kirashi ya karo mai,adadin yadda ake so, Daga haka mutumin ya kwashe kayan shi ya tafi yana mai zabga masu godiya, Inda maryam take ya dan kalla yana mai cewa ki kwashe su ki adanawa anty kafin ta dawo, Mamaki takeyi zuciyar ta,ace kaya masu yawa haka kuma kala guda,duk, za,a saye, koma na may ye oho, Sai kawai ta tsinci muryan Yusuf yana cewa duk wace tazo muna wanan farin cikin za a bawa Cikin mamaki tadan kalke shi kamar zatayi masu magana sai kuma ta bi umurnin shi tafara kwashe kayan zuwa saman wani kujera, Hira yaci gaba dayi shida Jibrin inda maryam takoma daki ita da yara har zuwa dawo wan su Anty dije, Bayanin da Yusuf kewa Anty Dije inda take sauraren shi a cikin mamaki, Turmin zani atamfa da kudi dubu biyar yabawa ko wace mace da tazo sha,anin bukin, Bakaramin mamaki Anty tayi jin wanan irin kyautar da yai wa mutanen ta, Don haka daya bayan daya ta dinga aika masu da alherin su gid kuma tana,sheda masu wanda ya basu, Ta aikawa iyayen mijin ta dashi da kuma, nata,uwayen Hakan ne yabawa baba daman kara tunawa da zancen shi na son ya hada zuri,a da wanan yaron, Saidai yasan cewa mutane zasu zarge shi da cew saboda abin hannun shi Yusuf din ne yake son yin hakan, , Amma dai shi in son samu ne yana mai son wanan abin ya tabbata, Bayan buki da kwana biyu Yusuf ya shigo gidan Anty inda ya samay su gaba daya zaune a falo, Ya saye cikin wata wagambari,mai ruwan sky colour, sai agogon da ya,daura, a hannun shi, Hular kan shi baka ce sai takalman kafar shi bakake, sai kamshin da ke tashi, Ganin su gaba daya afalon har mijin Anty wanda ya,shigo garin bayan kwana daya,wuce, Wani irin nauyin su Yusuf din yaji ,,inda yai, kamar ya koma baya, Amma sai mijin Ànty din yace mai haba dai kai,ko shigo mana, Yace haba dai Yusuf kamar wani bako can idan baka sake jikin ka ba har yanzu da Anty naka sai zuwa yaushe ? Maryam dauko mai cup mu karya tare, inji mijin Anty Dije yace wa maryam din Yusuf wanda kan shi na kasa bai daga ba yace wa mijin anty ai baya son tea so,sai yafi da, son ya sha kunu, shi, Da mamaki yake kallon Yusuf din inda yace kai kan iyalinka sun huta, gaskiya da wahala, Sai kuma yai saurin kai kallon shi ga Yusuf wanda ke shirin zama a lokacin yace Ya maganar zancen da Dije tace baba yai maku ne kai da maryam, naji shiru mana, Maryam wace a lokacin tana kokarin zuba mai kunun shi na gyada dake a cikin jug a cup Wani irin kallin mamaki ta aikawa Anty nata dashi wace itama dai mijin ta take kallo,, A hankali takai kallon ta ga Yusuf wanda shima kokarin sauke kai kasa yake yi, Jin gurin yai tsit ne yasa Illiya dagowa yai wa kowa kallon mamaki kai tsaye ya fara magana, Mijin Anty Dije ya kai kallon shi ga Yusuf din wanda kan shi ke a duke yace, Yusuf mu ba,zamu so, ace baku shirya dajuna ba kai da maryam , Sabo irin yadda muke tare da kai a matsayin dan uwa daga cikin mu, Don dai ita maryam nasan cewa bazata kyatare zancen mahaifin ta ba, Da sauri ta kara kallon mijin yar ta don jin abinda yace a kan ta, Don Allah ya Illiya ka taimaki rayuwata kasa baba ya janye wanan zancen, Wanda yake kokarin kwace min daga farin ciki na wanda nake kauna Wanan furuncin nata na karshe yasa,duk kan su kura mata ido, Yusuf wanda ke dan motsa kunu a cup ya ansa da cewa tabbas maganar maryam gaskiyane, Tunda tana tare da wanda take son tun da dadewa Kaga bai dace ace an rabata da wani ba dan wani, Wanan maganar da Yusuf yayi ta karshe shi ya,bawa mijin anty tausayi so sai May maryam ke nufi da cewa a bawa baba hakkuri sam bai taba zaton haka daga gare ta ba sam, Don haka cikin tsawa yadaka mata cewa baki da hankali a she maryam ina maki daukar mai hankali, ? To ki san da sanin cewa indai babane iyakar maganar shi ce ya fada ba wai zabi yabaki ba, Don ma dai kawai Yusuf din ya kasan ce shi bako ne daga cikin mu dakin ga aiki da cikawa, Hawaye ne ya fara silalo mata daga fuskan ta tana sharewa a hankali, Mijin Anty Dije yace ina ma wanda kikewa ikirarin cew kina dashi din yake, ? Maryam wacce saboda haushin irin yadda mijin yar ta yai mata a gaban Yusuf kamar wace ba tada gata, Yasa ko kallon shi ba tayi ba takama hanyar zuwa dakin takawai tana mai share hawaye, Tukin mota yakeyi amma hankalinshi na ga magganganun da sukayi da safe a gidan Anty Dije, A hankali ya shafa fuskan shi da tafin hannun shi, Inda ya hade wasu miyau masu daci da suka tsaya mai a bakin shi, Har ya isa garin Abuja maganar taki fita mai azuciyar shi, Bai huta ba ita kuma maman Choima ta haushi da fada akan cewa ya cuce su da ya aurawa Ibrahim da Naimat, Don may ya musuluntar da ita batare da sanin iyayyen ta ba, Dukan shi tsohuwar ta shigayi da hannun ta bibiyu tana mai yin kuka da ihu, Ganin zata iya bata mai lokaci ya sa shi janta a hankali zuwa dakin ta inda ya zaunar da ita a hankali saman gado yana mai ce mata ba gaskiya bane, Tace mai ai Samuel ya zo bayan baya nan yake sheda mata abinda ke faruwa, Sai da ya samu yadan lalabata ya wuce zuwa dakin shi, Rigar dake ajikin shi ya sabule gaba daya tare da jefata saman gadon shi, Shima fadawa yayi tare da lumshe idon shi yanamai karanto Subbahanallahi, Walhamdullahi Wallahu ,Akbar, Har zuwa lokacin da yaji zuciyar shi tai mashi sanyi, Sannan ya mike zuwa bathroom don yadan watsa ruwa, ko zai ji sanyi a rayuwar shi irin yadda yake ji, Sai bayan ya fito ne yana,saye da wata jallabiya mai ruwan milk, colour, Yana dan goge ruwa a kan shi wayar shi tafado mai a rai, Sai a lokacin ya tna cewa yasa ta a silent tun yana hanya, Da sauri yadauko wayar yana dibawa, kirane kusan talatin da wani abu, Inda akasarin su duk kurane daga anty Dije sai kuma sauran friend's da abokan aiki, Kiran karshe dayagani shi ya bashi mamaki don sam bai yi zaton ganin kiranta ba a wanan lokacin, Ba kowa bace illa maryam da mamaki yake kallon sunan nata yana mai tambayar kan shi ko may take so dashi har takira shi,, Wayan ya ajiye inda yanufi gurin da sallayar shi take yana kokarin shimfidawa, Karar wayar shi ce ta katse shi a lokacin don ya mai da ita da karar ta, Anty yagani rubuce a screen dinwayar tashi alamar itace ke kiran shi, Dauka yayi amma sai ta haushi da masifa tana mai cewa ina ya shige haka tun da safe take neman shi bata samun shi, Nan yake sheda mata cew yana Abuja kada ta damu, Cikin kwantar da murya tace Abuja Yusuf ? Abuja ka koma baka fada muna ba may yafaru Yusuf kawuce yau ba sallama haka, Murmushi yai mata a karo nafarko yau tun xa gari ya waye mai, Yace ba komai Anty tafiyar ce kawai ta riskeni a haka, Shirune yadan biyo baya batare dakowa yai magana ba daga cikin su, Kashe wayan yaji tayi abinda bai taba faruwa ba ke nan a tsakanin su, Yana kashe wayar kamar hadin baki kiran maryam na shigowa Amma sai ya share kiran nata kawai yatada sallah shi abin shi, Ya dade a zaune yana lazumi inda yake ta kai kukan shi ga Allah akan Allah yai mai mafita, da kuma zabi na alheri a rayuwar shi, Ya mike don ya kwanta ko zai dan samu barci yadan huta, Ya kwanta kamar minti biyar yaji kira ga wayar shi kokarin kashe wayar yakeyi a daidai lokacin da yaga sunan maryam again a saman wayar, Kamar ya share ta saidai yadaure ya dauka saboda time din da agogo ya nuna mai nadare, Muryan taji a cikin wani yanayi tana mai ce mai hello, Inda shima ya karba mata da cew wa,alakissalam, Sai kuma tai shiru batare da ta furta komai ba, Idon shi yadan rintse don wani irin abu da yake ji yana taso mai a zuciya, Yana niyar kashewa ne yaji muryan ta tana cewa Uncle dan Allah ka taimaka min agurin baba ka fada mai gaskiya cewa ba soyayya atsakanin mu ko kadan, Yanajin tafafi haka yakatse wayar tashi tare da rufe layin nashi yana mai runtse idon shi da suka kada sukayi ja,alokacin,,,,,,, l SEENABU ZEE MAKAWA YAURI KEBBI STATE,,, [4/7, 5:57 AM] ‪+234 810 770 2287‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAR YAURI, Alhamdullahi Rabbil,Alamin Ànty Dije tare da wasu daga cikin yan uwan su ne suka tafi kai amarya gidan ta dake a unguwar GRA, Motoci kusan biyar ne suka zo don daukar a maryan sanin cewa ba wai tana da wasu mutane da yawa bane a garin, So sai ko jama,a suka dan taru don zuwa rakiyar amarya gidan ta, da misalin karfe biyar na marancen, jumma,a, A bin gwanin ban sha,awa saboda irin yadda, mutane sukayi don Anty Dije, kusan duk wace take hurda da ita tazo mata wanan karar na buki, Amarya Naimat tasha ado a cikkn wasu lace farare kal dinkin buba, sai farin mayafi da kuma wani farin sarka mai daukan ido,sai wasu, fararen takalma a kafarta Idon ta alamar taci kuka saboda irin yadda sukayi mata wani irin lub, lub da su, Maryam ce kawai aka bari don tsaron gida tare da kau da sauran kayyayakin amfani da suka bari a waje, Sam bata san shigowar Yusuf din gidan ba saidai muryan shi da ta ji gab da bayan ta, Inda ta juya a yar razane cikin dan rudewa saboda rashin sanin mutum na kusa da ita, Fararen shadda ne a jikin shi dinkin tazar ce har kasa, Hannayen shi a harde saman kafadar shi inda ya kura mata ido kawai a cikin rashin sakin fuska kamar yadda yake a kullun, Sai da tayi kokarin saita kan ta,tukun, na san nan ta samu bakin yi, mai gaisuwa, Ya ansa mata kamar kullun a takaice sai dai na yau yana da dan banbanci da saura, Gurin fridge ya wuce direct inda ya bude ya,dauko goran ruwan Inuwa water, Kafa kai yayi batare da ya jira kofi ba, ya kama kwankwada, inda duk ya kwankwade ruwan tas, Yau she su Anty za su dawo ne maryam wace ke kokarin shiga store din su, dan aje kaya ta ansa mai da cewa, Anjima kadan shiru yayi ba tare da yakara magana ba , Gurin kujera two site ya nufa nan yazube sama yana mai cewa Ya Allah, Akawo ma abinci ne ta tambaye a cikin dan dari, dari, No thanks kawai yace mata inda ya maida idon shi ya kara lumshewa,, Aikin ta taci gaba da yi abin ta batare da takara bi ta kan shi ba, Yusuf wanda ke kwance tankar mai barci sai dai a zahiri idon shi biyu yana tunanen duniya, Wayar shi ce tai kara gurin da, yake aje a gefen shi, A hakali ya mika hannu shi ya dauki wayar sunan Jibrin ya gani, Dan gyara kwanciyar shi,yayi ya na mai kokarin daukar , Tambayar shi Jibrin yake, yi ko yana ina ne haka Sai da ya ja dan guntun tsuki kafni ya ansa mai wayar shi, tu kun, A takaice ya bashi ansa da cewa gidan Anty mana , Jibrin yai yar dariya kafin yai mai magana, tukun Da iskanci ai ba na fadama cewa zan dan gudo in huta ba kafin su dawo, Ansa yabashi da cewa an fa kawo kayan da ya ce akawo mai ga mutumin yana neman shi, Sai da yadan lumshe idon shi, sannan ya dan sukunyar da kan shi yana mai kallon ties din falon yace, Ya ce gaskiya Jibrin bazan iya zuwa in duba ba saboda ina hutawa yanzu, Amma zai iya kuzo nan ai maryam tana gidan sai ta tayaka dubawa, ko, Jibrin din ya ansa mai da cewa gashi nan zuwa tare da mutumin, Yusuf din ya ansa mai da cewa ya yi kyau sai kun ka raso ina ciki idan kunzo, A lokacin ne kuma su Assalam suka shigo gidan daga can cikin gida gurin kakan,nin su, Ganin yana bukatar hutu yasa maryam kiran yaran zuwa gurin datake, Aiko can gurin ta suka dan bata lokaci sai dai jefi,jefi tana kallon shi idon shi a lumshe suke, Ba ai wani dadewa ba Jibrin yai sallama tare da mai kayan, A kofar falo suka yi sallama maryam wace ke zaune da yaran suna kallon a wayar ta takarba masu sallaman su, Dukkan su a falo suka zube sai kayan da mutumin ke kokarin budewa daga cikin wani buhu, Zannuwa masu yawa tagani suna fitar wa daga cikin buhun, Jibrin din ne yasawa maryam wace ke ta waje kira, Sai da ta dan ja aji irin na mata tukun sannan ta mike zuwa ida suke, Tun daga nesa ya tsai da hankalinshi gurin ta irin yadda take tafiya, Tabbas maryam ta, tara abubuwa da dama da sai yanzu yake gani su daga gare ta, Idan ma don kyau ne ta na dashi uwa uba kuma hali duk yarinyar tana da,su, Cikin yaga da nuna isa ta yan matan taka ta iso gare tana mai cewa gata, Tankar ba shine yakare mata wanan kallon ba haka yanzu, Wayar shi kawai yake, ta famar tabawa ya Allah chatin yake yi ko kuma game, Jibrin ne yadan kalle ta yace ki taya mu zaben zani mai kyau daga cikin wa yan nan pls, Kurawa zannuwan ido tayi zuwa dan wani lokaci Sai ta jawo wani mai ruwan zuma, daga ciki yana da wani ado kamar gidan sugar Shi ta mika masu tana mai cewa wanan kamar yafi dama saboda baida ado da yawa so sai, Kai ya daga ya kalle ta da mamaki don jin cewa ra,ayin su yazo daya, da ita, Saboda tun da aka zube zanuwan idon shi yake akan wanda ta zaban Har zata juya don barin gurin saboda rashin sanin ko may za su yi da zannuwa haka, Muryan mutumin taji yana cewa zan,nuwan ai kudin su kaza ne, Dan juyowatayi tace wa mutumin kai malam fadi gaskiya yaushe kudin su ya kai haka, Jibrin yace wa maryam ta fada masu kudin kayan a takaice maryam tafada masu Amma kuma sai tace sai dai in har zasu bashi yadda yace ne saboda tai mako, Dariya duk suka agurin ban da Yusuf wanda dan murmusawa yayi inda ya bukaci mutumin da ya bashi turmi talatin, Yace idan basu isa ba zai kirashi ya karo mai,adadin yadda ake so, Daga haka mutumin ya kwashe kayan shi ya tafi yana mai zabga masu godiya, Inda maryam take ya dan kalla yana mai cewa ki kwashe su ki adanawa anty kafin ta dawo, Mamaki takeyi zuciyar ta,ace kaya masu yawa haka kuma kala guda,duk, za,a saye, koma na may ye oho, Sai kawai ta tsinci muryan Yusuf yana cewa duk wace tazo muna wanan farin cikin za a bawa Cikin mamaki tadan kalke shi kamar zatayi masu magana sai kuma ta bi umurnin shi tafara kwashe kayan zuwa saman wani kujera, Hira yaci gaba dayi shida Jibrin inda maryam takoma daki ita da yara har zuwa dawo wan su Anty dije, Bayanin da Yusuf kewa Anty Dije inda take sauraren shi a cikin mamaki, Turmin zani atamfa da kudi dubu biyar yabawa ko wace mace da tazo sha,anin bukin, Bakaramin mamaki Anty tayi jin wanan irin kyautar da yai wa mutanen ta, Don haka daya bayan daya ta dinga aika masu da alherin su gid kuma tana,sheda masu wanda ya basu, Ta aikawa iyayen mijin ta dashi da kuma, nata,uwayen Hakan ne yabawa baba daman kara tunawa da zancen shi na son ya hada zuri,a da wanan yaron, Saidai yasan cewa mutane zasu zarge shi da cew saboda abin hannun shi Yusuf din ne yake son yin hakan, , Amma dai shi in son samu ne yana mai son wanan abin ya tabbata, Bayan buki da kwana biyu Yusuf ya shigo gidan Anty inda ya samay su gaba daya zaune a falo, Ya saye cikin wata wagambari,mai ruwan sky colour, sai agogon da ya,daura, a hannun shi, Hular kan shi baka ce sai takalman kafar shi bakake, sai kamshin da ke tashi, Ganin su gaba daya afalon har mijin Anty wanda ya,shigo garin bayan kwana daya,wuce, Wani irin nauyin su Yusuf din yaji ,,inda yai, kamar ya koma baya, Amma sai mijin Ànty din yace mai haba dai kai,ko shigo mana, Yace haba dai Yusuf kamar wani bako can idan baka sake jikin ka ba har yanzu da Anty naka sai zuwa yaushe ? Maryam dauko mai cup mu karya tare, inji mijin Anty Dije yace wa maryam din Yusuf wanda kan shi na kasa bai daga ba yace wa mijin anty ai baya son tea so,sai yafi da, son ya sha kunu, shi, Da mamaki yake kallon Yusuf din inda yace kai kan iyalinka sun huta, gaskiya da wahala, Sai kuma yai saurin kai kallon shi ga Yusuf wanda ke shirin zama a lokacin yace Ya maganar zancen da Dije tace baba yai maku ne kai da maryam, naji shiru mana, Maryam wace a lokacin tana kokarin zuba mai kunun shi na gyada dake a cikin jug a cup Wani irin kallin mamaki ta aikawa Anty nata dashi wace itama dai mijin ta take kallo,, A hankali takai kallon ta ga Yusuf wanda shima kokarin sauke kai kasa yake yi, Jin gurin yai tsit ne yasa Illiya dagowa yai wa kowa kallon mamaki kai tsaye ya fara magana, Mijin Anty Dije ya kai kallon shi ga Yusuf din wanda kan shi ke a duke yace, Yusuf mu ba,zamu so, ace baku shirya dajuna ba kai da maryam , Sabo irin yadda muke tare da kai a matsayin dan uwa daga cikin mu, Don dai ita maryam nasan cewa bazata kyatare zancen mahaifin ta ba, Da sauri ta kara kallon mijin yar ta don jin abinda yace a kan ta, Don Allah ya Illiya ka taimaki rayuwata kasa baba ya janye wanan zancen, Wanda yake kokarin kwace min daga farin ciki na wanda nake kauna Wanan furuncin nata na karshe yasa,duk kan su kura mata ido, Yusuf wanda ke dan motsa kunu a cup ya ansa da cewa tabbas maganar maryam gaskiyane, Tunda tana tare da wanda take son tun da dadewa Kaga bai dace ace an rabata da wani ba dan wani, Wanan maganar da Yusuf yayi ta karshe shi ya,bawa mijin anty tausayi so sai May maryam ke nufi da cewa a bawa baba hakkuri sam bai taba zaton haka daga gare ta ba sam, Don haka cikin tsawa yadaka mata cewa baki da hankali a she maryam ina maki daukar mai hankali, ? To ki san da sanin cewa indai babane iyakar maganar shi ce ya fada ba wai zabi yabaki ba, Don ma dai kawai Yusuf din ya kasan ce shi bako ne daga cikin mu dakin ga aiki da cikawa, Hawaye ne ya fara silalo mata daga fuskan ta tana sharewa a hankali, Mijin Anty Dije yace ina ma wanda kikewa ikirarin cew kina dashi din yake, ? Maryam wacce saboda haushin irin yadda mijin yar ta yai mata a gaban Yusuf kamar wace ba tada gata, Yasa ko kallon shi ba tayi ba takama hanyar zuwa dakin takawai tana mai share hawaye, Tukin mota yakeyi amma hankalinshi na ga magganganun da sukayi da safe a gidan Anty Dije, A hankali ya shafa fuskan shi da tafin hannun shi, Inda ya hade wasu miyau masu daci da suka tsaya mai a bakin shi, Har ya isa garin Abuja maganar taki fita mai azuciyar shi, Bai huta ba ita kuma maman Choima ta haushi da fada akan cewa ya cuce su da ya aurawa Ibrahim da Naimat, Don may ya musuluntar da ita batare da sanin iyayyen ta ba, Dukan shi tsohuwar ta shigayi da hannun ta bibiyu tana mai yin kuka da ihu, Ganin zata iya bata mai lokaci ya sa shi janta a hankali zuwa dakin ta inda ya zaunar da ita a hankali saman gado yana mai ce mata ba gaskiya bane, Tace mai ai Samuel ya zo bayan baya nan yake sheda mata abinda ke faruwa, Sai da ya samu yadan lalabata ya wuce zuwa dakin shi, Rigar dake ajikin shi ya sabule gaba daya tare da jefata saman gadon shi, Shima fadawa yayi tare da lumshe idon shi yanamai karanto Subbahanallahi, Walhamdullahi Wallahu ,Akbar, Har zuwa lokacin da yaji zuciyar shi tai mashi sanyi, Sannan ya mike zuwa bathroom don yadan watsa ruwa, ko zai ji sanyi a rayuwar shi irin yadda yake ji, Sai bayan ya fito ne yana,saye da wata jallabiya mai ruwan milk, colour, Yana dan goge ruwa a kan shi wayar shi tafado mai a rai, Sai a lokacin ya tna cewa yasa ta a silent tun yana hanya, Da sauri yadauko wayar yana dibawa, kirane kusan talatin da wani abu, Inda akasarin su duk kurane daga anty Dije sai kuma sauran friend's da abokan aiki, Kiran karshe dayagani shi ya bashi mamaki don sam bai yi zaton ganin kiranta ba a wanan lokacin, Ba kowa bace illa maryam da mamaki yake kallon sunan nata yana mai tambayar kan shi ko may take so dashi har takira shi,, Wayan ya ajiye inda yanufi gurin da sallayar shi take yana kokarin shimfidawa, Karar wayar shi ce ta katse shi a lokacin don ya mai da ita da karar ta, Anty yagani rubuce a screen dinwayar tashi alamar itace ke kiran shi, Dauka yayi amma sai ta haushi da masifa tana mai cewa ina ya shige haka tun da safe take neman shi bata samun shi, Nan yake sheda mata cew yana Abuja kada ta damu, Cikin kwantar da murya tace Abuja Yusuf ? Abuja ka koma baka fada muna ba may yafaru Yusuf kawuce yau ba sallama haka, Murmushi yai mata a karo nafarko yau tun xa gari ya waye mai, Yace ba komai Anty tafiyar ce kawai ta riskeni a haka, Shirune yadan biyo baya batare dakowa yai magana ba daga cikin su, Kashe wayan yaji tayi abinda bai taba faruwa ba ke nan a tsakanin su, Yana kashe wayar kamar hadin baki kiran maryam na shigowa Amma sai ya share kiran nata kawai yatada sallah shi abin shi, Ya dade a zaune yana lazumi inda yake ta kai kukan shi ga Allah akan Allah yai mai mafita, da kuma zabi na alheri a rayuwar shi, Ya mike don ya kwanta ko zai dan samu barci yadan huta, Ya kwanta kamar minti biyar yaji kira ga wayar shi kokarin kashe wayar yakeyi a daidai lokacin da yaga sunan maryam again a saman wayar, Kamar ya share ta saidai yadaure ya dauka saboda time din da agogo ya nuna mai nadare, Muryan taji a cikin wani yanayi tana mai ce mai hello, Inda shima ya karba mata da cew wa,alakissalam, Sai kuma tai shiru batare da ta furta komai ba, Idon shi yadan rintse don wani irin abu da yake ji yana taso mai a zuciya, Yana niyar kashewa ne yaji muryan ta tana cewa Uncle dan Allah ka taimaka min agurin baba ka fada mai gaskiya cewa ba soyayya atsakanin mu ko kadan, Yanajin tafafi haka yakatse wayar tashi tare da rufe layin nashi yana mai runtse idon shi da suka kada sukayi ja,alokacin,,,,,,, l SEENABU ZEE MAKAWA YAURI KEBBI STATE,,, [4/7, 5:57 AM] ‪+234 810 770 2287‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA IYYA KA,NA ABBUD WA,IYYAKA NAS,TA, INN,, Dan Allah dai jama,a kuyi hakkuri dani saboda lokacina ne nake batawa ina faran ta maku rai dashi, Bawai dole yadda mutun yake so zai samu ba, Kuyi min Uzuri pls bawai magana daya nake ta fadi ba yadda labarin yake ne na,ke yi,,,, 👏👏👏👏👏👏👏 A,A ne zaune a gaban kanin mahsifin shi suna magana acikin na,tsuwa inda yake sheda mai cewa ya gama kammala duk wani abin da yadace da ake bukata, Ba musu kanin mahaifin nashi wanda ke shugabancin al,amarin shi. Sai yaron duk ta bashi tausayi don shi da a ce ya na da hali ne shi da kan shi zai wa yaron alheri, da duk wani harkan auren shi, Mutumin yace wa A,A din zai yi magana mahaifiyar shi, don ya shawo kan ta, Da haka sukayi sallama ya bar gidan kanin mahaifin nashi, Bai wani nisa da tafiya yakira maryam yana sheda mata cewa cikin satin nan za,a kawo lefen insha Allah, Duk irin yadda tayi kokarin boye farin cikin ta A, A sai da ya gane har yaji tausayin su ya kama saboda irin yadda suke son junan su Amma ga mahaifiyar shi tana kokarin raba su a lokaci guda saboda son rai, Maryam batai kasa a gwiwa ba ta sheda ma yar uwar ta abinda ake ciki, Maganar Anty Dije ta saurara amma tasan cewa ba wai lalai ne hakan ya yuwa ba, Don haka sai bata dauki zancen da wani mu,hinmanci ba kawai sai ta share zancen, batare da ta fadawa kowa ba, Kwana kamar biyu da zancen wanan kanin mahaifin na A, A ya samu mahaifin Maryam, tare da wani dan uwan su akan zancen, Inda baba ya sheda masu cewa subari sai ya ga yarinya tukun, Daga haka kawai,bai kara wani zamce ba amma sai may kamar sati guda da magana da wani yammaci sai ga mata dauke da akwatina, har guda uku da kit din su, Abin ya bawa anty dije mamaki kwarai da gaske, a inda ta aika makwabtan su akakira mata wata kawar ta, Matan sai wani yatsinar fuska suke yi kamar masu jin wari ko ka,zanta, Da farko ita Anty Dije bata so ta karbi kayan ba don bata da masaniyar komai akai, Amma sai wanan kawar na ta tace mata su karba ba,a haka, nan, alheri baizo ma a gida ka kore, Ba wasu kudi masu yawa anty ta bazu tukuici ba saboda rashin sanin zuwan su a lokacin, Su ma dai ana su bangaren su fita da,sunan Anty Dije a bakin su kan cewa ba masu wani taron arziki ba, Can suka koma gidan suka samu shi A A din kowace daga cikin su da nata abinda tace mai akan wai bai samu diyar gidan mutunci ba, Ga su diyan tallaka am.a suna ma mutane kallon rainin hankali, Duk maganganun da,suka fadi a gamay da maryam din zu zafe shi a zuciyar shi, Saida bai ce masu komai ba sai sauraren su da ya dinga yi a lokacin, Amma yana barin gurin su ya sa waya ya kirata sai abinda bakin shi yaraga mata yana cewa wai an wulakanta mai yan uwan shi Ita ko maryam sai hakkuri take bashi tana cewa gaskiya basu fadi daidai ba saboda tasan cewa ba halin Anty Dije bane haka nan, Don haka sai ma taga cewa shi ai bai ga laifin nashi ba sai yar ta kawai, kashe wayan tayi tana mai mugun jin haushin matan da sukai masu wanan mugun kazafin, Tun wanan lokacin sai bata kira A,A din ba shi kuma haka, dakewa tayi dashi, Bayan wasu kwanaki suna zaune a tsakar gida saman wata katuwar tabarman roba zaune, suna shan iska, Kasan cewa garin yau babu wutar ne fa zafi yai masu yawa, Bayan sallah isha,i zaune take tana lazumi inda yaran Ànty ta ke ta faman damunta da surutu, Muryan Baban su ne su,kaji a cikin wanan daren, Take gaban maryam ya tsinke ya fadi. Gaisuwan baba suka fara yi suna mai sannu da zuwa, Maryam wace bata san ko may yakawo mahaifin nasu ba acikin wanan daren, Da sauri ta mike zuwa shimfida mai tabar don ya zauna, Har zata wuce gurin da take zaune da farko bayan ta gama mai Muryam baba taji yana cewa dakata samu guri ki zauna, don tafiyar ki ce wanan Turus tayi waje guda tana mai za,zare idanun ta a lokacin, Kanta ta sun kuyar kasa har zuwa lokacin da Anty ta ta karaso gurin, Da ga can gefe guda ta dan samu ta zauna tana mai addua acikin zuciyar ta A hankali ta daga kai ta kalli yar ta wace ke kokarin zama a kusa da ita Kanta ta maryam kasa don ganin canzawan da fuskokin su yayi a lokaci guda, Gyaran murya baba yayi kamar kullun idan har ,ai yi magana mai muhin manci Ya,soma da adduan koran sheda da kuma fatan alheri a gare su, Sannan Baba ya soma da cewa dalilin wanan kiran shine don in fadakar daku in fada maku abinda ba,ku sani ba yau, A hankali maryam wace kanta ke a duke ta dan dago ta kalli su anty da baba, sai kuma ta mayar da kanta a kasa, Baba yace maryam ina son ki saurare ni da kyau ki ji may zan fada maki akai, Yaron nan dan gidan yan masuga da kikaturo min iyayyenshi, Kwanakin da su ka wuce, nace su dan dakance ni akan wani bincike da nake son yi, Kawai tun ban ai,watar da komai ba sai ga zance daga yar uwar ki cewa wai sun kawo kayan lefen su, Sai kuma baba yai shiru hakan yasa gurin yai shiru kamar ba kowa agurin, a lokacin, Ina son ki san cewa maryam duk da ban da komai "ya ta ba yar babyn roba bace haihuwar ki akayi kamar kowa ce "ya, dake garin nan, Hawayen da yake bin fuskan tane tai kokarin sharewa a lokacin Maryam baba ya kira ta da wani kakausar murya yace mata Ina son kamar yadda kuka tsara kawo kayan ku ke da shi to haka kuma zaki, kara sheda mai cewa ya aiko wa yanda ya turo su kwashe mai, Wani irin kuka maryam tasa mai tsuma zuciya inda baba ya ce kaiyya, Ta yaro kyau take bata karko, Wanan yaron da na zaba maki bawai na fasa zancen shi ba ne don kin ji cewa nayi shiru, Duk wani bincike da uba yakamata yai wa mai bidan diyar shi nasa an min tun tuni akan wanan yaron dan gidan na masuga,, Gaskiya ba zan iya bada diyata wanan gidan ba sam, Saboda wasu dalilai, da nagano akan su da kuma kwata kwata ni dai bai min ba, Kara dan sautin kukan ta tayi a lokacin saboda jin hukuncin da baba ya yanke a,kan ta, Sai kuma ya sasauta harshen kadan yace ke maryam in banda abinki, wanan yaron ai abin tausayawa ne, a gare mu, Dago kai tayi don jin abinda baba yace tadan kalleshi a cikin mamaki, Taci gaba da cewa, kowa a garin nan yasan cewa baida gidan zuwa wanda yafi nan, Yau ai abin kunya ne ace muna nan har ake mai gorin mace, Wanan kawai bai isa mu wani ishara ba aiko da ace banda "ya ta cikina zan zagaya ko a cikin dangi in samo mai, Balle gani da ku har ku hudu a gida ke ce kawai ko a gidan nawa zan iya bugun gaba da ke batare da raina ya baci ba, Shiru yayi na dan tsowon lokaci, kadan sai kuma ya goge hawayen shi, Abinda ya tayar wa maryam har Anty Dije da hankalo ke nan, suma kukan su ka fara yi, Baba cikin muryan mai kuka yake cewa sam ban tsanmaci haka ba daga gare ki maryam Sannin cewa da kikayi bazan iya cutar dake ba a matsayina na mahaifinki, Idan har akwai wani da da nake so da tausayawa a cikin gida maryam bayan ki ne, Badon komai ba sai kasancewar baki da uwa a cikin gidan Allah ya taimake mu ni da ke yaba mu Dije a matsayin uwar tayarwan ki, Cikin muryan kuka maryam ta dago kanta tana mai cewa baba ni bance ba zan yi ma biyayya ba, Amma wanda kake kokarin hada ni da shi shine duk yan uwan shi kafirai ne Arna Wa yan da ba su sallah basu kuma da niyar yin ta ako da yau she, Kafin ta kai karshen maganar ta baba yace kin ko ga idan ki shiga gidan shi kun zama ku biyu ke da shi, Hakan zai sa ya rage kuncin rayuwar da yake ciki na yan uwa da rashi shakikin abokin shawara, Anty Dije wace sai yanzu ta gane hikimar baba na wanan hadin da zai yi wa maryam da Yusuf, Baba yace maryam kin san wanan yaron da dadewa kuma kina da masaniya daga wasu daga cikin halaiyar shi, Kin ga ke nan abin zai zo maki da sauki don saboda sanin abubuwa da dama dakikayi a kan shi, Yakare da cewa masu, kinga mu, wanan ne kadai gata da mutuncin da zamuyiwa Yusuf maryam, a irin yadda ya rike mu, Maryam wace ta dago kai acikkn mamakin mahaifin ta wanda ke tausayawa wani bare bisa ga ita da take yar shi ta cikin shi, Cikin kuka tace baba niko halin da zan shiga fa idan har an min haka, Haushi ne ya kama baban don jin abin da yar nashi wace yake tinkaho da bugun gaba da ita, Batare da ya bata ansa ba ya mike tsaye saboda takaici yana wa wanan shi hukuncin da na yan ke akai, bana son in kara jin komai, Idan Allah ya kai mu lokacin mun dawo sai mu fara zan ce auren insha Allah, Daga haka ya fita batare da ko ce madu mukwan lafiya ba kamar yadda ya saba ce masu a kullun, A,zaune ya bar su kowa jikin shi a mace tun dai maryam wace ke ta sharban kuka alokacin, Don jin cewa yau za,a raba ta da masoyin ta abin kaunar ta A,A, Shigowar shi gida ke nan a gajiye daga office da kyat yake dan iya cira kafan shi saboda gajiyan da ya kwaso Don yau su Alhaji sambo sun shigo garin tun da safe suke zaune a na wasu lissafi akan harkokin business din su, Saman kujera guda ya samu yazube gaba daya maman Choima wace ke zaune daga gefen shi guda ta wani kalleshi a yatsune ta kauda kan ta gefe, Saboda wani irin matsanacin haushin Yusuf din da takeji a yanzu, Yamai da kan shi musulumi yakuma mai da diyar mutane dake zaune a karkashin shi, Pipkin ne ya sheko da gudu daga dakin da ya fito, Yazo ya fada mai ajiki yana mai oyoyo da dawo wan uncle din shi, Rugumay yaron yayi tsam a jikin shi yana mai jin wani feeling akan yaron Shi har kullun wanan yaron tausayi yake bashi a irin yadda zai tashi ya rayuwa babu mahaifi a tare dashi, Kara rungumay yaron ajikin shi yayi ya dauke shi cak zuwa saman dining table, inda ya dire shi, Sai,da suka kammala cin abincin su ya kira Nani din shi taje ta kwantar da shi saboda school da safe, Shima a gajiye ya haura sama don yadan watsa ma jikin shi ruwa, Wayar shi ce dake rike a hannun shi yaji tana ruri, Bakuwar noba ce yagani don haka sai bai dauki kiran da wani muhinmanci ba, Sai bayan fitone daure da alwala don ka,idan shi ce yin hakan, A lokacin da yake sallah ya dinga jin wayar ta shi kira nata shiga, Sai da ya idar yadauko wayan misscall goma sha daya yagani duk da noba guda, Sai da ya zauna yakira mai wanan nobar da bai san ko waye ba, Bakuwar murya ce yaji wanda bai san kowaye ba, ya karba mai sallamar shi,, Tambaya yayi ko waye a layin tare da shi don bakuwar noba ce a gare shi, Ansa aka bashi a dayan bangare da ce wa, hello don Allah da Joseph Emanuel nake magana, Murmushi yayi kawai inda ya karba mai da cewa eh dashi kake magana, Ok inji mai wayar yace kana magan da Aminu ne dan gidan, masuga dake a unguwar jankidi, Look Joseph ina son sanin inda yaron da Ejoma ta taba haihuwa ne yake,? Shin macce ce ta haifa ko namiji ina kuma yaron yake, ? Tsuki Yusuf yayi baiko gama jin bayanin ba ya kashe wayan , Komawa yayi bakin gado yazauna ya mai harde hannayen shi a cikin juna, Maganganun da,wanan guy din yayi a lokacin ne suke dawo mashi a rai, Abubuwan da yace a gamay da Naimat din a wancan lokacin sune abinda ke mai yawo akai tankar yanzu akayi su, Mikewa yayi zuwa downstairs dakin da Pipkin ke kwance ya turo a hankali, Inda ya hango yaron a kwance cikin sleeping dress din shi fare masu dan adon pink colour, Tsayawa ya yi daga kofan daki kafan shi a harde yana ma yaron wani kallon cikin tausayi, Yasan dama something wrong zai faru da yaro din shi yasa duk kwanan na yake yawan tunanen al,amarin yaron, Yadade gurin yana kallon dan yaron dake kwance dunkule a saman gadon shi yana barci,,,,, Maryam wace ke jin cewa duk duniya ba mai son ta a wanan lokacin saboda babu mai kaunar farin cikin ta ashe, Ba wanda yafi bata mamaki ga wanan al,amarin kamar Anty Dije wace, taki aiwatar da komai akan zancen, Don a zaton ta Anty Dije zata iya shawo kan mahaifin ya yi hakkuri da zance hada ta da Yusuf da baba ke kokarin yi, Idan har suna ganin cewa baba ya zai hada tane da Yusuf don wani ra,ayin kan shi to lalai sunyi kuskure sosai, da yin hakan, Ita dai sam zuciyar ta yaki amincewa da zance Yusuf din akanta, Mutumin da tun tsawon sanin shi da tayi babu wani zancen so ko makamanci soyayya a tsakanin su, Shine yanzu za,a ce wai ta aura a matsayin mijin auren ta, Yusuf din nada abubuwan da mata da yawa ke so a gurin namiji a rayuwar su, Amma ita sam wa yan nan abubuwan basu burgeta haka kawai take jin tsanar sa, Yanzune ma da suke dan sabawa a hankali tarage jin wanan tsanar da take mai, Wanda tun farko ya samo asaline tun lokacin da yake dan mabiyi addinin Christian, Tun alokacin take jin batason al,amarin shi a rayuwar ta, Wasu hawayen ne masu zafi suka kara zo mata wanan karon, bata damu da wai ta goge su ba,daga fuskan ta ba,, Jin alamar shigowar mutum a dakin baisa maryam wace ke kwance tana sharban kuka, dagowa ba, Gefen gadon ta samu ta zauna takai wani lokaci ta kurawa kaunar nata ido sosai, Tawani ramae acikin dan kankanin lokaci, tayi baki ga kukan da tasawa kanta duk ya wani kumbura mata ido, Duk da farko tausayi take bata yanzun ganin da tai mata yasa ta jin tausayin ta sosai,,,, SEENABU MAKAWA, [4/7, 6:57 AM] ‪+234 703 981 8283‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 6⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA MA, LLIKI,YU,MMIDEEN,,,,, BARKAN MU DA JUMMA,A YAN UWA MUSULMAI,,,ALLAH YA SADA MU ALHERIN DAKE A CIKIN WANAN RANAN ALLAHUMA AMEEN👏 Hannun ta takai a hankali tadafa yar uwan nata dake a kwance tankar wace bata a cikin hankalin ta, Sautin kukan na, ta ne tasake gaba daya a lokaci guda,, Jawota Anty Dije tayi zuwa jikin ta itama hawaye takeyi saboda tausayin yar uwar ta, Murya irin ta mai kuka Anty Dije tace, Maryam ki daina wanan kukan haka kada ki jawa kanki matsala, Don dai kin san halin baba ko waye, mutun ne wanda bai magana biyu, Kamar yadda ta fada maki cewa ke din tausayin ki ne yake ji har yasa kika samu fagen mai musu, Ina son ki kwantar da hankalin ki kin sai dai cewa aure na Allah ne ai, Kika sani cewa ko wani matsala yazo ya hana ayi auren, Kamata yayi ki barwa Allah zabi akan al,amari ba wai ki kama butulce mashi ba, irin haka da kike yi, Maryam sam banso tun farko har ki bari Yusuf yagane cewa ba kya son shi ba, haka, Shima da ba wai baba ne ya haife shi ba ya daure ya nuna boyewar zuciyar shi, Don may ke da baba ya haifa zaki kasa daurewa ki nuna biyayyan mahaifin ki, Sai a lokacin ne maryam ta dago idon ta dake face face da hawaye ta kai kallon ta ga Anty nata, Anty yakike son in yi da abin da raina baiso Anty ban taba jin cewa ina son uncle da soyayya ba arayuwata, tun farko, Daukar shi nayi a cikin mu tankar wani dan uwar mu, Amma Anty taya za, ace wai ni dangin mijina duk kafirai ne, Da sauri Anty Dije ta dafe mata baki kafin ta karasa zancen ta, Da cewa Assha maryam kin san abinda yasa Allah yai wanan hadin a tsakanin ku, Kin sani ko shigar ki cikin su zai kawo sanadiyar musluntar wasun su, Maryam Yusuf mutum ne wanda ke bukatar mace wace zata ba shi kulawa, Saboda yana cikin maraicin rashin yan uwa na sahihi a tare da shi, Yana son mace mai mutunci da sanin ya kama tane bawau irin wa ancan matan da suka laje mai don kwadayin dukiyar shi ba kawai, Wani irin kallon tuhuma maryam ke aikawa Anty ta don jin wanan maganar da ta,jera a lokaci guda watau ke nan Anty ce ta ke son wanan hadin ko ? Saboda son Yusuf din da takeyi tan,kar wani jinin ta can, Wai may yasa Anty Dije take son al,amarin wanan bawan Allah haka ne,? Muryan Anty ne ke cewa maryam kinfi kowa sanin cewa bawai don abin hannun Yusuf nake ra,ayin shi ba, ko ke da shi, Tadan girgiza kanta cikin ban tausayi ta ce kawai don kyawawan halaiyan shi ne na alheri, Wanda tun farko na hango su daga gareshi amma baida mataimaki, Kanta takawar daga kallon yar nata, a lokacin da taji haka din, Wani irin bakin ciki ne ya tokare mata zuciyar ta ta rasa yadda,zatayi da,shi, Komawa tayi da kanta saman filo tana mai kallin silin din dakin a hankali ta lumshe idon ta saboda tuno wasu abubuwa da dama a zuciyar ta da tayi,,,,, Kusan kwana nawa Yusuf bai kira yan dattijan da suka maye mai gurbin mahaifin shi ba gurin sa ma albarka da fatan gamawa da duniya lafiya, Mahaifin jibrin ne ya fara kira inda suka gaisa a cikin ladabi da biyayya, Sun dan kai wani lokaci yana mai bashi hakkuri da duniya, da mutanen cikin ta, Sai kuma malam Abdulsamad da yakira shima kusan irin yadda sukayi da mahaifin jibrin ne sukayi da shi, Sai kuma yai niyar kiran mahaifin Anty Dije wanda dattijon ke burge shi saboda irin halaiyar shi na sanin mutuncin mutane, Da gaisuwa ne suka fara magana da mahaifin na su Anty Dije, Inda yake mai magana kamar nasiha akoda yaushe, Anan yake sheda mai cewa ya yi kokari ya shigo ya duba mahaifin shi, Ya daina dadewa baizo gurin shi ba saboda hakkin mahaifa ya na a kan shi, Sosai Yusuf yaji dadin wanan nasihan na baba shi yasa shi har kullun yake sun al,amarin wannan tsohon, Ya kai wani lokaci, azaune gurin da su ka gama waya da mahaifin su anty dije din, Hannun shi bibiyu ya tallabo haban shi da su yana mai tuna nen yadda zasu kwashe da mahaifin shi, Murmushi yayi shi kadai don sanin cewa sai sun kwasa da mahaifin nashi, Wanda har zuwa yanzu bawai ya hakkura da zancen shi bane, Amma ya zai yi dole ne ya bi zancen dattijon nan don neman albarkan,mahaifa, Ta gama shirya duk wani abin dazata bukata acikin yar jakar ta mai kama da handbag, Kaya kala ukune tsab ta tura ciki sai yan abubuwan bukata kamar su, kayan shafawa, irin na mata da unders, Wani katon hijab fari ta zunduma a jikin ta ta yadda ba mai iya gane cewa ta na dauke da wani abu a jikinta Tafiyan ta a cikin natsuwa tare da dan jan aji kamar kullun, Kokai waye ka ganta sai ka kara wai,gawa don ganin ta, Can hanyar fita gari maimashin ya kai ta don ta tare motar da zai kai ta garin Bobi Ana Sallah Azahar ta isa garin bobi inda ta samu jama,an gidan nasu mahaifiyar ta lafiya kamar kullun, Duk sunyi farin cikin a ganin maryam din saboda jimawan da tayi bata zo garin ba, Mahaifiyar dai kallon ta kawai take yi batare da tace mata komai ba, Amma dai rayuwan ta ya bata cewa ba tafiyan lafiya yar diyar nata tayo ba, Su biyune adakin yanzu tana zaune daga gefe ta na kallon yar diyar nata, Daketa wasa da spoon a cikin abincin da kishiyar ta tasa asayo mata, abakin kasuwa, Sunan ta, ta, takira har sai,da maryam din ta dan zabura sabboda nisan da tayi a cikn tunane, Yar baba mai ke tafe dake ne haka a wanan lokacin, Maimakon tai magana sai kawai tasa kuka kamar zata suke, Bata cewa yar nata komai ba illa fita da tayi zuwa, dakin kishiyar ta, Can sai gasu tare su biyu sun shigo dakin,hankali a tashe,sai kallon ta sukeyi, Da kyat kishiyar ta tasamu Maryam ta tsakaita da kukan nata,, Nan dai cikin hikima suka samu har maryam din ta dan labarta masu irin abinda ke tafe da ita da , Salati suka sa a lokaci guda suna mai, tafa hannyen su don mamaki, Mahaifiyar ta ce ke cewa yar baba ina maki daukan yarinya mai hankali ashe ke ba haka kike ba sam, Hankalin ki bai kai ba sam to yanzu mai kikazo gurina in maki, In goya maki baya ki bijirewa mahaifin ki ko may,? Kirufawa kan ki asiri tun muna mu biyu ki koma inda kika fito, Kishiyar mahaifiyar ta ce ta dakatar da mahaifiyar na tada cewa ya isa haka ki bari abi a hankali, Haba yaya zuwa tayi don ta ja min magana ga dangi, mu kawai ta barna min suna, Kishiyar mama ce tace barin kira malam ina ga zaifi sauki, A tare suka,shigo da malam mijin mama wanda fuskan shi kawai zai nuna ma cewa baiji dafin abin da tayi ba, Maryam wace sai kuka takeyi a lokacin bata iya cewa komai don gaba daya yanzu tagane ba,a son ta kowa sai Yusuf, Daga karshe dai shawara ya yanke akan cewa ta koma ita kadai batare da,wani ya rakata ba don kada agane cewa guduwa tayi, Mijin mama yai mata nasiha sosai akan cewa tayi hakkuri da zabin mahaifin ta insha Allah bazata tabe ba, Maryam tana share hawaye da gefen hannun ta ta mike jiki ba kwari don bin umurnin mahaifan ta, Anty dije bayan tadawo ne ta laika ko ina bata ga maryam ba , Sai abin yabata mamaki saboda sanin cewa maryam dun ba ma,abociyar fita bane duk sanda taga dama, Har gidan makwabciyar su ta leka da taji shiru amma sai matar tace aiba ta, shigo ba, Hankali ta yakara tashi sosai amma sai bata kawo komai ba a ran ta, Don haka tamike da, kan ta don yi masu girkin abin da za suci a ranan, Har zuwa yamma ba maryam don haka hankalin ta ya kara tashi sosai, Jin ana kiran sallah magarib ko ina yasa ta kara tsinkewa, Alwala tayi da niyar yin sallah idan ta idar sai ta shiga gidan su gurin baba, ta sheda mai, Da sallamar ta tashigo gidan ta wuce dakin ta direct ta kwabe hijab din ta da sauri kamar yadda kishiyar mama ta ce mata tai saurin mayar da kayan ta gurin da suke, Buta ta sura zuwa gurin alwala, sallah magrib ba, din kada ta makara, Tana zaune bayan ta idar fa sallah tana lazimi taji shigowar yar nata, Daga kofa ta tsaya tana mai tambayar ta da cewa ina ta tafi tun da safe, haka,? School muka,shiga don yin submit din wani takarda, dake a hannun mu, Amma maryam shine baza ki fada min ba sai ki bari ina yawon neman ki, Kiyi hakkuri tace kawai sai anty dije ta juya batare da takara cewa komai ba,,,,, Sosai wanan karon yai shirin shigowa don yasan cewa lokacin tafiyan Alhazai ya yi Insha Allah, Shigan dare yaiwa garin a lokacin don haka bawai kowa ne yasan da zuwan shi garin ba,, Gidan mahaifin shi ne ya nufa kamar yadda baba ya bashi shawara, Zaune Mr Ema yake yana shan hantsi, safe dake karawa,jiki karfi, Cikin mamaki yake kallon dan nashi ganin irin yadadda ya kara zama big man Da gani abin duniya akwai su a gurin sun zaunu dam, Duk irin yadda ya sha cewa zai dake aduk inda suka hadu da yaron nashi ya gwada mai cewa ya fita batun shi sam, Zaune yake amma Yusuf din yana zuwa yadan rakwafo zuwa jikin mahaifin nashi kadan, Bayan shi yadan bubuga yana mai baya yana ce mai welcome my Son, Ba karamin mamaki Yusuf din yaji ba don jin abinda Dad ya ce mai yau, Yaushe rabon shi da samun haka daga gare shi har ya manta da lokacin gaskiya, Hamdala yayi azuciyar shi na samun wanan sassaucin da yayi gurin mahaifin nashi, Bayan sun gaisa ne yakoma mota ya,dauko mai tsaraban da yazo mai da su, Daga gidan nasu yakama hanyar zuwa gidan anty dije, Gittawan motar shi da suka gani ne yasa su gane cewa ya shigo gari a lokacin, Aminu wanda ke tsaye a kofan wani shago ya ji ana cea cewa Dan iyamurin nan yashigo kenan kwanan nan akwai harka ke nan, Cikin sauri Aminu din ya juya don yagan shi wani irin yai mai acikin mota yake zaune, Binshi yayi da kallon mamaki har ya bace mai da gani, don yasan cewa tunkar shi akan a kan yaron nashi zaiyi wuya sosai,, Gidan Anty ya yaron nashi daniyar zuwa ya karya zancen dan shi yanzu yana da wuya sosaiduk da yasan cewa bawai ansan da zuwan, n shi bane don haka ba,a yi komai dashi ba, sai dai yasan cewa bazai rasa mutumin shi ba ai watau ,kunu, Duk da safiyane, Wasu Swiss pure cotton ne saye a ajikin ta masu saukin kudi, ne amma sun karbe ta sun kara fitar mata da kyaunta Kunnun gyada yau suka dama saboda yaran sunce shi suke son sha, wannan lokacin, Sallamar shi ce yasa yaran kurma wani irin ihun murna, a lokacin, a Wanda ya jawo hankalin iyayyen nasu gare su, kowan su sai da yai mamakn ganin shi Maryam wace tafito daga kitchen dauke da cups a hannun ta ganin Yusuf a tsaye tare da yaran yasa ta tai kamar ta koma baya Sai kuma tadake takaraso tana mai sannu da zuwa, Sau guda ya dan kalli gefen da take ya kau da kan shi cikin sauri, Amma sai yaji gaban shi yai wani irin faduwa saboda ganin yadda ta koma takara yi mai wani fes a fuska, ZEEE. MAKAWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Dan girman Allah ku tayani addu,a pls ina a cikin damuwa, 👏👏👏 IYYA,KA NA, ABBUD,DU WA, I YYAKA NAS,TA,INN, Kusan maryam ce ta karshe gurin yi mashi sannu da zuwa, A lokacin tana dauke da cups din kunun yaran guda biyu a hannun ta, Mikawa ko wani yaro nashi cup din tayi ta juya da niyar komawa kitchen din, Muryan Yusuf ne wanda ta dade bata ji ba yake cewa, Maryam da akwai sauran kunnun dan Allah a san min, Guri guda ta tsaya cak don sauraren a binda yake cewa, Tana kokarin juyawa ne don ta debo mai, sai, taji muryan Anty Dije a bayan ta tana cewa, Haba Yusuf azubo maka dai ko badai a san makaba, Dariya yadan yi mai kama da yake yana cewa to ba, a dama shi da ni ba aikin ga zan rage maku quantity ko? Zama Anty Dije tayi suka fara gaisawa yayin da maryam ta nufi kitchen kawai, Tafe take dauke da tire da jug din kunu sai kuma wani giran ruwa mara sanyi da ta azo a sama, Saboda shi da kan,shi ne yai mata bayanin cewa Idan mutun yasha kunu mai zafi ko tea baya shan ruwan masu sanyi don gudun kamuw da cancer ciki, Hakan yasa indai abu mai zafi zata kawo mai sai dai ta dauko ruwan da ba, sa a fridge ba, A gaban shi ta aje tire din wanda dukawar ta yai daidai da juyowan shi, da sauri ya kau da kan shi gefe guda, Saboda shakan numfashin juna da sukayi, inda turaren ta yadaki hancin shi, Itama dai maryam daurewa tayi saboda mayattacen turaren shi mai dafe wa mutun a hanci idan ya shaka, Duk taji kamahi shi har yabar gari da kusan yan kwanaki zakaji falon gidan su yana wanan kamshin nashi, Jiki ba lakka ta juya da niya barin su amma kuma sai anty ke ce mata maryam wainar zamuyi ko an fasa ke nan, Yusuf wanda ke zuba kunu a ciku. Cup yana jin an anbai waina sai cewa yayi masha Allah har na manta raboda masa, Yar harara maryam ta watsa mai ta wutsiyar ido tace, Cikin wata irin narkarkiyar murya Anty da dai mun barshi kawai ayi wani abin, Daga Anty har Yusuf dariya sukayi saboda sun gane nufin ta, Anty Dije tace maryam ke muguwa ce ko don kin ji kanina yace yana son ci zaki mai kurulla akai, Sai kuma jikin maryam din yai sanyi don an gane nufinta, Sai cewa tayi nifa Anty ba don shi nace haka ba gani nayi dai kamar baza aci bane kawai, Waye ba zaici ba maryam abin da muka kwana da niyar yin shi sai dai in kece kika fasa ci din, Maryam ta juya jiki ba kwari ta fada kitchen girkin miya tafara dorawa tukun, Miyan kaji ne yaji agushi, sosai a cikin shi sai kuma ta dora farfesun kayan cikin rago a dayan murhun, tafara yin hadin masa,, Sosai masan yai kyau don tunda dare ta jika danyen shinkafa a ruwa bayan ta gama hada miya, sai ta je ta tsamay shinkafan a ruwa tasamu wani roba mai marfi ta sa aciki, Ta dauko flower da yis da baking powder ta zuba ta dan sa ata rudu danye kadan sai kuma yan gurorin shinkafa kadan, Almajirin su da ke masu wanke, wanke da yan sauran aiyuka tabawa yakai mata nika, Kafin ya dawo ta dauko man suya da duk wanin abin da zata bukata na masa a kusa da ita, Ba,a wani dade ba yaron yadawo daga gurin nika nan maryam ta zauna tafara suyan masan Yayi fari yai kyau ba tsami ko kadan kuma yafita za kyau, Sai da tagama soya masan sanan ta koma takan farfesun da take yi na kassan rago, Kusan lokaci guda ta kammala komai ta ajiye, a cikin kula, Daki su ta fada tai wanka takara fitowa wata fes da ita, kamar ba itace tai wanan aikin ba Azaton Yusuf maryam ba zata yi masan ba ne don baiga tana da niyar yi ba don haka ya mike yana cewa Antyn shi, Shi zai tafi idan ta gama masa zai dawo anjima yaci, Anty ce take ce mai ai har angama ko tun,dazun ko, Maryam anty takira don ta zubawa Yusuf masan, kafin ya wuce, Duk a zaton shi ko wasa sukeyi mai sai kawai yaga shigowan maryam dauke da kulolin abinci, Mamaki ne yakama shi don ganin har maryam ta canza shigar ta, ashe daga dogon riga ta koma zani da riga yar atamfa, Ghana, din dan dagwas a jikin ta, Ta durkusa gaban shi tana kokarin aje kulolim abincin, da ta shigo da su, Idon shi fes a fuskan ta don har ya manta da cewa anty na gurin, Anty dije tamike tana cewa maryam dan Allah zuba mai ibda leka nan gidan hafsat yanzu zan dawo , Yadda anty tabarta a durkushe tana kojarin aje kulun hakan ne ya bashi daman karewa maryam din kallo, Lumshe idon shi yayu ya koma saman bayan kujeran yadan kara bayan shi,akai, Kamshi turaren da tasane ya shiga hancin shi sosai ya shake shi ya koma bude idon shi da sauri, Cikin wani irin murya maryam taji maganar shi a kunnen ta yana cewa acikin lumshe ido kamar na mai jin barci kin yi kyau maryam , Kamar a mafarki taji wanan maganar don bata taba zaton jin haka gare shi ba, Sai kuma ya daure fuska tankar bashine yai wanan maganar ba, Daga kai tayi cikin jin nau,yin shi sai sukayi ido biyu da junan su, A sanyaye maryam tace mai tana mai bude kulalan waina taje tanbayar shi guda nawa zan sa ma a plate, Baki ji may nace bane maryam yakara tambayar ta ido a cikin ido, Hawaye ne ya gan garo daga cikin idon ta zuwa fuskan ta,a hankali, Saida ya dan lumshe idon shi yadan hade wasu miyau da suka tsaya mai a wuya, Sanan Yace, haba maryam bana son ganin kin bata wanan kwaliyar da hawayen ki Fitan hawaye daga idon ki tankar rage wani sanadari ne daga cikin jikin ki, A sanyaye cikin murya kuka tace uncle kayi hakkuri kai wa baba magana a kai na pls, Ido ya kura mata a lokacin da take wanan maganar, Ji yayi tankar ya rungumota ba don komai ba sai wani irin mugun tausayin ta da yake ji a lokacin, Sai dai a gaskiya bazai iya yiwa mahaifinta musu ba kamar yadda yaga tanayi, Ita kanta yasan dalilin yin hakan nata bai wuce irin halin da surutun mutane zai jefa ta a ciki bane na yadda da auren shi da zatayi, Don har yanzu al,umma suna mai daukar bai musulunta ba don basu daina nuna mai kyamar kabilanci ba, Amma sai kawai ya nuna mata cewa shi din na mijine kuma babbane don hakane ya yi kokarin tursasa wa zuciyar shi son ta har kuma zuwa yanzu din yaji cewa ya kama da son ta din, Don haka ayanzuma yarinyar tausayi taba shi ta re da jin wani irin mugun sha,awan ta da son ta kamar ranshi zai fita, Haka kawai wanan ganin da yai mata yadinga jin wanan bakon yanayin a gamay da ita, Ya dan rintse idon shi na dan wani lokaci sai kuma ya bude su still maryam tana durkushe a idan take , Ya mika hannun shi a hankali yadafa hannunta dake a saman kulan dake gaban ta, Jin hannun shi a saman nata yasa tadan cira kai takai mai kallon ya hakane ? Ya kalle ta a san yaye don shi da kyat yake bude su, yace Maryam tun ranan da baba yai muna wanan zancen baikara ce min komai ba a kai, Amma ke har yanzu kinki bari zukantan mu su zauna lafiya akan zancen Maryam ta kara runtse idon ta lokacin da taji yace mata hakan ga,din, Kenan ma ahida ba mahaifin shi ba yai biyayya akan zancen sai itace mace kuma diyar ahaifinta wanda shi yakewa ikirarin yaiwa biyayyan akan maganar shi,baba din, Zuciyar ta takama mata sake,sake a lokaci guda ta rintse idon ta akaro na barkatai dan tsugunin ta a,gurin, Wani irin damuwane yashige ta alokaci guda har ta dan dinga jin zazzabi na satan ta, Kallon ta yayi cikin tausaya mata yace ki tashi maryam kada kafan ki yai ciwo, A hankali cikin raunan,nan murya tace barin sakama masa a plate tukun, Ya ce to nagode maryam da kulawar ki insha Allah biyayyan ki bazai zama na banza ba, Taci gaba da zuba mai miya asaman masan da tasa mai kwara uku, Ta mika mai tare da jawo cup din ruwa agaban shi tana kuma bude mai kulan ferfesun kassan ragon da tayi, Hannun shi ne ya dan kara taba nata ida daidai lokacin da take kokarin tashi a gurin, shi kuma zai dauko spoon, Tsikan jikin ta ne ya tashi yarrra ta zamay a hannkali gami da mikewa don barin gurin, Kallo Yusuf ya bita dashi har zuwa kofan fita falon da ta nufa, Kitchen takoma ta gyara sauran kayan da ta watsar gurin hada mai abincin, Falon ta leka ko yagama sai dai ta sha mamakin ganin ko kwaya biyu bai iya cinyewa ba yana ci a hankali, Tambayar shi tayi da cewa ko masan bai mai dadi bane a baki , Bai amsa mata tambayar taba sai dai bude mata kulan dake agaban shi ya yi sai taga ya cinye fiye da rabin masan, Mamaki maryam tayi don sam bata san zai iya cin masan ba,, sai gashi yabuge ga cin yawa, Har zuwa lokacin da ya gama cin abincin anty bata dawo ba, Dama ya riga yagane plan ne yasa ta fita tabar su, Tambayar ta ya yi da cewa ke bazaki ci abincin bane, ? Duk da wani irin mugun nauyin shi da kunya da takeyi, Kai kawai ta iya dan girgiza mai ba tare da tai magana ba, Mikewa yayi ba tare da yai mata wani magana ba yanufi kofan fita daga falon, Saida yakai kofan fita batare da ya juyo ba yace mata na gode sai an jima ko? Inda ya fita yabar ta rakube anan gurin antyn ta tasamay ta tazubar da hawaye, Kallon ta tayi cikin tausayawa yar uwan nata, tambayar ta takeyi ko may ya faru, Tana share hawaye take girgiza kai gami da furtawa a hankali da cewa ba komai, Yasha kwana round about da zai kai shi unguwar sabon gari , Sai ji yayi ana kokarin tsaida shi kamar kada ya tsaya saboda a saman hanyane gashi naida security , atare da shi duk da yasan cewa, ba,abinda zai faru da shi acikin garin kwantagora yanzu din, Guri ya samu yai parking din motar shi a hankali ya sauka saman titin, Fuskan da yagani sai yake tunanen ko a ina ya san shi, Gaisuwa sukayi acikin mutunci inda yake tamayan Yusuf din da cewa yazo lafiya? Lokacin da ya,ke ko karin tambayan shi kowaye shi, Sai yaji mutumin na fadin kamar baka gane niba,ko ? Ga kwanaki nai ma waya akan zancen Cikin da Ejoma tayi, Wani irin kallon mamaki Yusuf ke binshi dashi sai cigaba da fadi mutumin ya yi , Ina da tun farko ka fada mincewa duk wanda ya aure ta zaka kashe mai wanan dukiyar aida an aure dani, YUSUF ke mamaki a zuciyar shi irin yadda wanan mutumin ke maganar shi wani kamar mara hankali, Yanzu so nake idan da akwai abin da ta haifa har zan karba, Sai kai min wani dan ihi sani kaga sa in toshe bakin duk wani wanda zai kawo min cikasa ga ala,amari,,, Zaici gaba Yusuf yadaga mai hannu yanna na cewa ka kai ni koto ina ga zaifi , Ya juya kawai abinshi batare da ya ji mai zai ce mai ba ya shige motar shi ya bar gurin, ZEEE MAKAWA YALWA [4/10, 6:23 AM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI AL,HAMDDULLILAHI RABBIL AL,LAMIN ADDU,AN KU AGARENI NAGODE SO,SAI YAN UWA MUSULMI IRIN YADDA NAI TA GANIN SAKON TAYANI FATAN ALHERI, NAGODE MAKU KWARAI DA GASKE, ALLAH UBANGIJI YA BIYA DA ALHERIN SA👏 Tukin mota yake amma zuciyar shi ta na gurin tunanen halin rayuwa irin na Aminu masuga, Duk da yadda yake daukar kan shi bakon shiga cikin addini Kamar yadda mutane da dama ke mai wanan fahinta, cewa bai san komai ba akan addini tukun, Hakan ba zai sa shi yin wani abinda zai kas,kantar da kanshi gamay da addinin shi ba irin haka, Mutum yasan cewa ya aikata zina amma saboda rashin sanin kaidar sharia har yana ikirarin cewa idan za, a bashi wani dukiya mai tsoka zai iya fitowa fili yai ikirarin cewa shike dan da yai rejecting da farko, saboda kwadayin duniya kawai, Kan shi ya girgiza don takaici da abin da wanan guy din yai mai yau, Allah ya kyauta ya furta a fili ya na mai ajiyar zuciya shi kadai a mota, Saboda sanyin da jikin shi ya yi bai iya zuwa gidan su Jibrin da yai niyar zuwa ba a lokacin, Don haka juyawa yayi zuwa gidan shi don ya dan samu natsuwa, Maryam wace ke zaune ta zubawa plate din da ta zuba ferfesu a gaban ta ta kasa koda kai cibi biyu a bakin ta Tun cibin farko da takai tasamu ta hadiye shi da kyat saboda sam bakin ta batajin dadin shi ko kadan, alokacin, Sai dan daukan spoon din tayi tana dan juya,shi a ha kali, amma ta kasa kaiwa a bakin ta, Wayan ta ne yai kara inda taga A,A ne ke kiran ta alokacin, Sai da ta juya inda anty dije take zaune taga cewa hankalin ta baya gurin ta, Sai ta mike a hankali zuwa dakin ta inda zata fi jin dadin sake jiki tai waya, Bayan ta anty dije tabi da kallo mai kama da harara, ta sake dan guntun tsaki tace a fili mara hankalin yarinya kawai, Zama tayi saman gadon ta a hakali tana mai ansa mai sallama, Muryan shi taji yana cew may yasa may ki maryam naji muryan ki wani iri daban, Ba komai ta furta ahankalin sai ta baka tausayi idan kaganta a lokacin, Don har idon ta yakawo hawaye ko tankar zasu zubo mata, A zuciyar ta tausayin kasu takeyi don ta san cewa raba su za,a yi, bada dadewa ba, A,A ya sheda mata cewa zaiyi tafiya sai bayan kwana uku zai dawo, har ma ya fara hanya ko, Duk da rayuwan maryam din ya baci don rashin sheda mata cewa zai yi tafiyan da bai yi ba da wuri sai bayan ya fara hanyar tafiyan shine zai kirata ya sheda mata, Fatan adawo lafiya tai mai inda take ce mai Allah ya bada sa,an tafiya ya karba cikkn dadi rai da cewa Ameen nagode tawa, Bayan sunyi sallama ta kashe wayan takai wani lokaci zaune inda take tana tunanen irin rayuwan A,A narashin sani darajan abokin zama, Ku san ko yaushe haka yake mata wanan halin wani lokaci ma sai ya kai inda zai tafine zai kirarata ya sheda mata, Safiya ta nuna mata rashin faidar irin wanan halin amma so ya hana taga lain malam din nata, Kiran sallah dataji anayi na la,asar yasa ta aje wayan tamike don zuwa dauro alwala, Anty dije ce a waje take ce mata, zancen zuwa dibo Naimat da sukayi ta shirya anjima idan Yusuf ya shigo sai ya kai su saboda safe yara zasu school, Bata rai tayi don sam batajin dadin irin haka da anty ke mata tana wani cucusa ta ga Yusuf, Gidan Naimat ne za,ace sai ya kaisu ita da yara, saunawa tana zuwa ita da su a saman mashin, Matsala guda dai yanzu shine dan fitinar hawa mashin yana gari, zai sa mata ido, Rai a bace ta ansa ma yar ta da cewa aida abari kawai weekend sai mutafi mu yini mata ko ? Maryam kece fa kikace kun yi da ita jiya zaku zo ayau din ko? Bata kara cewa komai ba don tasan ceqa ba yarda Anty zatayi da wani excuse din da za ta bayar ba, Tuwon semo da miyar yauki sukayi don Yusuf dake agari kawai in badon yana gari ba suna da sauran abinci da zai kai su har dare, Sai kuma gashi yau din Yusuf din baiwani yawan shigowa kamar yadda yake yi ba idan har yana gari, Jibrin ne yakira shi a waya yana mai complain akan KB wanda yanzu sam ya canza sosai, Har zuwa lokacin da Jibrin din yakai karshen maganar shi Yusuf bai ce mai ufan ba, Sai ma murmushin da yai mai alokacin da yaji cewa ya kai karshen korafin, Yace Jibrin kafi kowa sanin halina a halin yanzu , Nai maku hanyar wanan business din ne don ku samu madogara har ku taimaka ma wasu daga cikin mutanen ku, Tun a wanan lokacin ni ban kara damuwa ko wani irin hali kuke ciki ba , Idan har nace zan dinga bin didigin may kuke ciki da aiyukan ku ke nan badon Allah natai maka maku ba. So kamai don Allah kafita batun shi kasa mai ido kawai , nadade da sanin irin halin da yake acikin tun lokacin da yai aure, Addua kawai nake mai akan Allah ya sa ya gane gaskiya batare da yafada acikin halakaba Kaiwai mu bishi da addua kaji pls ka dai na yiwa dan uwanka mugun fata, Tsigar da yake magana ne yasa Jibrin jin wani irin nauyi don shi ya,kamata ace yai wanan maganar amatsayin shi na dan uwa kb da sukafito cikin kabila daya, Nan yake shedawa Jibrin cewa ai yana kwantagora saboda yana son yai spending din sometimes with his Dad, Wanka ya fada don ya dan ji dadin jikin shi ko zai rage jin kasalan da yada may shi, tun dazun, Wasu kananan kaya yasa wando da riga duk bakake sai kwalar rigar ce kawai ke da ja, Kamshi turaren shi na THE da JOJOBA yana nan kamar kulun, Saida yafitane yasamu yadan ba masu gadin shi wmai dan ihi sani kamar yadda ya saba yi masu idan yazo, Su ko sai addu,a suke zabga mai tankar yau yafara masu irin haka, Indai har yana gari to sun yake talauci ke nan su sai dai kuma in bayan ya wuce, Maryam wace a lokacin tana daki zaune tafito daga wanka tana saka riga don shiryawa saboda tasan cewa yau fita dole akan ta,,,, Muryan shi taji yana sallama tuni zuciyar ta ya tsinke, saboda addu,an ta na fatan kada ya shigo bai ciba, Muryan yaran Anty Dije taji suna mai sannu da zuwa tare da fada mai cewa zai fita da su da little Mum, A tsorace maryam ta sake tsaki saboda yawan suruntun yaran da yai yawa, Tau fa zuwa ina da daren nan yake tambayar yaran, Suna hada baki gurin cewa gidan Anty Naimat, zamu tafi tare da little mum Wani murmushi yayi mai sauti yana cewa cikin daren nan zaku bazaku bari da safe ba, No, Uncle inji Assalam gobe akwai school bamu zuwa ko ina, Idan mun fita sai na gama zan je nadauko ku ke nan, Tsigar da yake maganar shi yasa yanayin maryan jin tsoro don tasan ceq zai zube su nan ne yatafi nashi tsabgar, Idanu ta zare don tagona manufar zancen shi da sauri ta kalli agogo inda taga takwasa saura na dare, Muryan anty ce ya katse ta tana cewa wai ina maryam ta zuba ma abinci, Da sauri ta karasa daurin dankwalin dake hannun ta tun kafin anty ta balbale ta tafito, Karan daurin zanin ta ne dake bada sauti idan ta taka yasa shi daga lumssasun idanun shi yadan dubi gefen datake tafiya, Wasu shaddane jikin ta masu ruwan makuba dinkin fitted ne anyi aikin wuta akai an darza wasu duwatsu kanani suna walkiya, Sai wasu takalma plat masu dan tudu kadan adudugen su, Ganin shi zaune a cikin falin nasu alokacin yasa tai mai Sannu da dawowa tace mai a takaice ta wuce abinta zuwa kitchen, Mamakin iya kwalliyan wanan yar karamar yarinyar yake yi, Yarinyar duk yadda tai kwalliya sai ya burge mutum, Already abincin yana a cikin kula don haka daukowa kawai tayi takawo mai inda yake zaune, Kai maryam har kin ban tsoro da,wanan kulan naki , Masan da naci dazu baiko gama aikiba fa yadda yai maganar saida kowa falon yai dariya har maryam din dake ta faman daure fuska, Harara maikama da murmushi ta sakar mai ta gefen ido tace aiko tunda munyi dole kaci shi uncle, Assalam ya jowa yana cewa zo ka tayani my son kada in kasa ccinyewa ni kadai, Bayan tagama zuba mai dan kadan tamike tsaye ahankali tana mai kokarin wuce, Sunan ta yakira a hankali yana mai langabar da kan shi cikin marairaicewa kamar dan karamin yaro ya na mai cewa haba little Mum ai wanan yai muna yawa, Mikewa tayi gami da dan mai hararan wasa wanda yakarawa fuskan ta kyaun kallo, Tace cikin yar murya irin nata, You have to eat, it ,all so pls excuse me, Da sauri Yusuf wanda sam ya manta cewa anty Dije tana gurin yai niyar kamo ta cikin wasa, Maryam wace a zaton ta dagaske kamota zai yi sai ta dan zille mai tayi waje tana dariya , Wanan abin yasa anty dije cikin farin ciki amma sai tai kokarin boye farin cikin nata agaban su, Don haka sai ta nuna cewa bata fahince shi ba takawo wani zance na daban, Kwalaben turaren wuta anty bawa su maryam sukaiwa Naimat din, Inda Yusuf koda bai gani ba afili yai murna sosai irin yadda yaga tana kokari da yar uwan nashi, Wakan secret lover's ke tashi a motar inda Yusuf ke marming a hankali, Yana tukin motar tankar wanda bai son tukin alokacin, a hankali,, Wayar shi ce tai kara inda yaga kb ne bai fi minti biyar ba yakashe wayan, Sai kuma ga kiran Jibrin ya shigo again, kamar hadin baki, Yadai mutumina yace da ya dauki wayan, alokacin wankan dake tashi bai bari suji may yake cewa, Amma dai taji lokacin da yake cewa gani nan da su maryam za mutafi unguwa, Batasan ko may yace mai ba sai murmushin da taga ya dan yi, Fuskanta na gefen widow tana sauraron abin da mawakan ke fadi gamay da secret loves, d two hearts dat beat together, Kaman kada ya gama wayan sai wani irin annashuwa yazo mai a lokaci guda, Muryan shi ya kashe ta yadda yaran dake bayan motar baza su iya jin ko may yake cewa ba Maryam ya ambato cikin muryam maikama da wanda ke rada, yace, Kiyi hakkuri da ni pls duk da nasan cewa bai kai matsayin da zaki soni a zuciyar ki ba Badon komai ba sai don kasan cewa na tankar FUREN KAN JUJI, Don banda wasu yan uwan da zan gwada wa alumma inyi alfahari da su, acikin su, Kinga kuwa hakan zai sa duk wani mutum mai raunin imanani ya ji kyamar hada wani alaka dani kamar yadda iyayyen Sadiya sukai min ikirari da hakan, Abin mamaki sai maryam taga kawai hawaye wasu na bin wasu a fuskan shi Abinda bata taba gani ba a rayuwan ta taga namiji na kuka haka, Itama maryam haka kawai batasan lokacin da hawaye wasu na bin wasu afuskanta cikin kukan tace may injiwa Ni uncle bana kyamar yan uwan ka tunda mahaifana basu kyamace ka ba tun farko, Cikin murya maikama da rada tace kawai dai malam A, A da mukayi nisa da shi nake jiwa, Murmushi yayi daidai lokacin da zasu karya kwanar da zai sada su da unguwar su Naimat, Hasken motane ya hasko mata motar A, A din tare da wata yarinya a tsaye hannu rike da na juna, Yana saye da wani dinkin shadda light green Ganin hasken yaimai kau a lokaci guda yasashi kokarin kate fuskan shi da hannayen shi, Gaban maryam ne yabada damm kardai A,A karya yai mata dama, A zaton maryam Yusuf baigane cewa A A din ta bane can suka wuce, a baya, Wayan ta ta jowo takira layin wayar shi, tambayar shi tayi da ya isa lafiya ko? Ya amsa mata da cewa a,a lafiya kalau har ma na kwanta, ZEEE MAKAWA YELWA [4/10, 6:23 AM] 0mmer Farouk: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI IY,YA,NA,A ABBUDDU WA,IYYAKKA NAS,TA,INN, Duk da ga hasken street light's da ya haske ko ina a titin da kuma hasken abin wuta da ke gittawa jefi jefi a lokacin, Baisa idon maryan ganin haske ba alokacin, magana Yusuf ke mata amma sam bata ji may yake cewa ba , Sai ji tayi yana cewa idan kun shiga kada ku dade zan dan je in dawo pls, Hakan ne yasa ta gane cewa sun iso gidan su Naimat din ke nan, A hankali ta sauka motar batare da ta dauki ledar sakon da Anty ta bata takawo ma Naimat ba, Yusuf din ne bayan ta sauka ya miko mata ledae yabata takar ba a darare, tawuce zuwa cikin gidan, A lokacin yaran da suke a tare har sun isa ciki ko sun ririke Naimat din, Sun sami Ibrahim a gida don haka bawai wani sake jikin ta tayi ba, Saboda dama hankalin ta baya tare da ita a lokacin, Ganin yanayi da maryam ke cikine yasa Na,imat dan maida hankalinta gare ta, Saidai maryam din tayi kokarin yin dariya irin ta yake din nan, Fira sukeyi amma zuciyar ta ya,gurin abinda idon ta ya hasko mata, dazun nan, Sakon da,aka basu ne sukawo wa Naimat maryam ta bata tai mata bayanin akan ko wanin su sai wani mugun kamshi ke ta shi,,, Nan Naimat din ta dinga jin dadi saboda wanan sakon da akai aiko mata, Sun kai kamar minti talatin Yusuf yadawo inda yakira ta layin wayar maryam din, Tare suka fito da Naimat don ta gaisa da Yusuf din wanda har zuwa yau bai taba shiga gidan Naimat din ba, Itakan maryam karfin hali kawai takeyi a lokacin saboda abinda tagani yau karara cin amanar da kusan ko da yaushe safiya ke fada mata cewa A, A cin amanarta kawai din ya keyi, Amma ita sam so ya hana taga gaskiyan hakan da ake fada mata Magana sukeyi amma acikin yaren su na IBO ne don haka maryam takoma jikin mota ta dan jingina jikinta a kai, Saboda irin yadda take jin kafafunta baza su iya daukanta ba, Kallo guda zakai mata zaka ne cewa babu kwanciyar hankali a tare da ita alokacin, Shigar su mota ba,wanda ya kara yiwa wani zancen komai kowa da abinda yake sakawa a zuciyar shi, Sun shiga gida tana tsaye tanawa anty bayani sakon Naimat amna sam Anty ta kula da cewa bata a cikin hankalin ta , Ledojin da Yusuf ya sayo masu kaji gassasu da kuma drinks masu sanyi da tsada, Sai wasu kayan tarkace su sweet da sauran su biscuits, kala, kala har leda biyu, Gudan ledan dagani tarka cen maryam ce a ciki amna lokacin da anty Dije ke ce mata tazo ta dauki nata sai cewa tayi anty tabarshi a gurin ta, Tasa kai kawai daniyar shigewa dakin su, batare da ko ta juyo ba, Anty Dije cikin haushi take cewa maryam wai ke wata irin yarinya ce mai taurin kai, Dan Allah ki duba wanan yaron bai fasan ko mu suwaye ba Allah ya hada mu dashi har yake muna irin wanan biyayyan tankar wasu yan uwanshi na Jini, Ke ko duk kin bi kin takurawa wa rayuwar ki, Kin hana rayuwar ki farin ciki, kullun a cikin tsangwamar kan ki da tashin hankali, Maryam kan tana daki zaune saman gadon ta sai hawaye takeyi na takaici, A haka ranan ta kwanta ko kayan jikin ta ta kasa cirewa kafin ta kwanta,, Zaune yake inda ya idar da sallah walha kamar yadda ya saba yi, Jikin shi saye da wata bakar jallabiya mara hannuwa, Zaune yake a takure yana jan casbi da hannu guda a hankali, Wayan shine Jibrin din ya kira shi yana,cewa ga,shi ya taso zuwa KG din shima, Nan dai sukayi sauran bayanin irin abinda zai zo mai da su na bukata wanda bai samu sayowa ba, Suna sallama da juna sai abinda yafaru jiya da dare ya fado mai arai, Ashe bayan ya aje su maryam gurin da A,A yake tare da wanan yariyar yar makarantar su ya koma ya samay shi, A hankali yafito daga cikin motar shi daya dan Parker nesa kadan daga inda suke, Tafiyan shi irin na gogagun matasa yan bariki da yake ko yaushe har yazama mai jiki, shi yakeyi ya tun,karo inda suke, Da farko bai gane ko waye ba sai da Yusuf din ya zo gab da su yagane cewa shine, Hannu ya mika mai don su gaisa amna sai Yusuf din yaki sai dai ce mai da yayi sallamu Alaikum, May yasa baku zantar da gaskiya a cijin rayuwa mai karya zai haifar ma arayuwa, Yaudarar diyan mutane tankar wani taki ne da mutun ke zuwa bawa acikin gonar shi, Don duk abinda ka shuka sai ka girbi abinka ga hannun ka, Yauda gobe dama masu karin magana sunce sai Allah, Yariya ta dauki amana da gaskiya tabaka amma kai ashe yaudar ta kakeyi, Ko da yake itace dai dama bata san da haka ba amma ai duk wani wanda ke tare da kai yasan da hakan, Don ruwa ba saa,n kwando ba ne , Dakata malam inji A, A yake cewa ina ruwanka da rayuwata da har zaka zo kana min irin wanan nasihar haka kamar wani malami, Tubabbe irinka da bai ko iya karanta fatiha ba har zaka zo kace ni zakaiwa wa,azi, Tun,da kai kagane cewa ina cin amanar tane ai in ka isa sai ka hana ta kulani, Ko kafada mata cewa ga irin yadda nake ko ya kare yana wani shu,umin dariya, a karshe, Azaton shi ya kashewa Yusuf baki ba zai iya cigaba da maganar shi ba, Yusuf yai mai wani irin kallon na baka da mutumci yace ai ba sai na fada mata ba, Don tagani da idon ta kuma tai kokarin confirming ko da gaske yaudarar ta kayi sai katabba tar mata,da hakan din, So Wait and see what Will happen, Ya juya kawai yabar gurin cikin kunar rai irin yadda musulmi dan uwar ka zai ma gorin addini ku, Lumshe idon shi yayi yana mai jin kunar irin tozarcin da ake yawan yi mai akan zaman shi cikin musulmai hausawa, Murmushi ya yi gami da,wani irin shu,umin murshi daya biyo bayan na farko, Daga haka yamike zuwa bathroom don yai wanka yafita zuwa gidan Dad, Anty Dije taimamaki acikin zuciyar ta jin maryam na cewa zata gidan su safiya tunda farar safiyan nan, Murmushi tayi don tasan cewa, akwai dai saboda Safiya ce indan tazo kullun korafin ta shine maryam bata da zumunci, Zaune take a dakin da aka warewa safiya da kannen ta acikin dangidan nasu mai gina irin na local people, Hawaye wasu na bin wasu, ita ko,safiya wace ke zaune gefe acikin tashin hankali sai hakkuri take ba, Duk da maryam din ta kasa magana balle ta fada mata abinda yafaru yasa ta wanan irin kukan haka, Sai da ta,samu ta dan tsa,kaita kukan ne tafara tambayar ta ko may ke faruwa, Sannu a hankali ta zayyanawa safiya yadda sukayi da A A din daren jiya, Har saida takai karshe safiya tana sauraren ta bata ce komai ba alokacin, Murmushi safiya din tayi da tagama jin may tace, Ta ce gwada da Allah ya gwada maki kika gani da idon ki, Ai yanzu zakiyar da da cewa dan iska ne macuci mayaudari, Fuska a,daure maryam ke kallon ta tace ke nan ma ke kin dade dasanin kowaye shi ko, Safiya tace tun yaushe maryam ai shima yasan nasani saboda acikin office din shi na kama,shi, red,handed, Ido waje Maryam ke kallon Safiya don jin abin da tace, nan dai safiya ta bata labarin cewa taje gurin shi don tai mai magana akan takardun ta, Shi ne ta samay shi tare da wata yarinyar yar IBO suna kiss, Na shiga uku maryam tace tasake wani sabon kuka alokacin, Safiya tace rokona yai tayi dan Allah in rufa mai asiri kada in bari ki sani ki, ki shi, Harda alkawarin kudi yai mun nace mai ban so yadai daina abinda yakeyi, Ni a lokacin maryam ke ce ke bani tausayi ina gudun kuyi aure ya dauko maki cutar kanjamau, a karshe, Rinanun idanun ta da suka sha kuka sukayi jawur,da su, tadaga tana mai kallon safiya da su, Tace cikin wani irin muryan kuka mai ban tausayi Safiya malam ya cuce ni wallahi, Sai dai nagode ma Allah da daidai da rana daya bai taba nuna min true colour din shi ba, Safiya tace ai kin san cewa yai min aike matar aure ce su ko wa yan nan na rayuwar waje ne kawai, Safiya tadan dafa ta tace ki godewa Allah da bai sa yakai ga cuta maki rayuwa ba, Kawai ki fita batun shi kiyi fatan Allah ya baki wanda yafi shi nan gaba, Wani sabon kuka tasa ta shige jikin safiya saida tayi mai isar ta, Ruwa safiya takawo mata ta wanke idon ta dashi sai faman ajiyar zuciya takeyi akai akai, Duk yadda safiya taso su karya a tare maryam din taki don haka ta kyale ta kwanta sai barci mai nauyi ya kwashe ta abinka ga wanda baiyi barci ba adaren jiya, Wayan ta yai kara safiya tadauka azaton ta ko A, A din ne tai mai tas sai taga ashe Anty ce, Waje tafita don ta sheda mata tana barci hankali anty ya kwanta don jin lafiya maryam din take,,,, Zaune suke a tangamaymayn falon su na gidan mahaifin shi dake dauke da jibga,jibgan kujerun da Yusuf ya sa masu da dadewa, Mr Emanuel wanda ke zaune cikin shiga irin ta IBO, da,wani abu kamar zani ko buje daure ajikin shi, Sai da yadan kurba ruwan Lipton din aka dafa mai as usual sanan ya kali inda Yusuf yake zaune yace mai, Kada ka man ta da maganar da naima duk Christmas atare da mu zaka yi shi, Yusuf yai yar murmushi kafin yace ai ba matsala saboda addini na ya yarda min da in shiga church don wasu yan dalilai, Na ku daine sam ba a yarda ya,shiga muna gurin bautar mu ba saboda tsarkin sa, Dad sai da naje Jerusalem na fara gane ce wa Muslim suna gaba da mu sosai saboda duk irin abinda sukeyi shine mutum zai yi acan, Daga Alwala da kuma sa tufafi masu daraja sai cire, takalma don shiga cikin churches din, Zaici gaba da bayani Mr Ema wanda tunda Dan nashi yafara bayanin abinda yagono a Jerusalem, yake ji tankar yana zuba mai ruwan zafi ne ajiki, Duk da yasan gaskiyan maganar ke nan Yusuf ke fadi, Yadaga mai hannu a lamar ya isa haka, bai son jin kareshen zancen, Murmushi Yusuf yayi don yasan cewa gaskiya yake zaiyano mai baidai son jin zancen ne Ga mamakin Mr Ema sai yaga Yusuf yadauko cup ya dan tsiyaya ruwan litop din yana kurba a hankali suna hiran business, Inda mahaifin nashi ke fada mai cwa yanzu business din shi bai gane komai akai, saboda yaran dake gurin macutane, Yusuf baiji dadin jin hakaba don haka yai alkawarin zai diba al,amarin company yai gyara akai, Sai zuwa wani lokaci yai masu sallama ya nufi gidan uwar dakin shi, Anty Dije, Bai wani dade ba a gidan don rashin ganin kowa yara,suna makaranta, maryam kuma bata gidan, Don haka sai yaji gidan yai mai girma kamar bakowa a cikin shi, Abubakar dan Anty Dije ya lake mai ya shuri yaron suka fita, tare, Gidan man mahaifinshi yanufa inda yaje ya dan fara bincike akai,,, Maryam wace yuwa yatayar badon taso tashin ba ta mike ba shiri a lokacin kusan karfe biyu saura, Alwala ne taje ta dauro tazo tayi sallah,sai a lokacin aka shigo mata da wani kula green da plate guda biyu, Danwake da mai da yaji ne da yankakken salad yasha kayan hadi, Safita takaraso dakin bayan kaunar ta da tashigo da jug da cups a hannun ta, Sosai tasamu taci dan waken ba kadan ba saboda tana,son shi dama, Sai bayan sallah la,asar ta shirya tafiya zuwa gida Zuwa dan a lokacin ta dan sake jikin ta, ba kamar yadda tazo ba, Tafe suke da mai mashin din, da ya dauko ta daga, Usubu, uguwar su Safiya, Suna tafe mai mashi na ta zuba mata surutu maryam wace sai addua, takeyi a bayan mashin Allah ya kai su lafiya don surutun yai yawa, Yusuf wanda yake tafe daga gidan man mahaifin shi da ya ziyarta, Kamar a mafarki yaga maryam a saman mashin, Wani irin mugun mamaki ne yakama Yusuf din Maryam akan mashin duk da ya ce mata baya so, Sosai ya take motar ya cin masu, tana saye da wandon Jen's da wata yar riga karama pink sai katon hijabin da tasa, a sama, wanda baka gane irin kayan da ke a jikin ta, Saboda mashin din da ta hau sai wandon Jen's din yafito don ta tattara hijab din kafatan saye da wasu plat shoes mai belts, Horn yai masu amma sai mai mashin din yai zaton cewa ana masu ne don su kauce, a hanya, Karo nabiyu da ya kara yi da karfi yasa su wai gawa har maryam din, Fuskan shi daure tamau a cikin glass din motar da yake a ciki yana ja, Kallon da tai mai kawai yasa ta fahinci mai yake nufi, Cewa mai mashin din tayi ya sauketa inda a hankali Yusuf yazo gab da ida take ya Parker motar shi, Shiko mai mashin sai kallon ikon Allah yakw yi kawai wanan irin tsaleliyar motar ga kuma mai tukin tankar bature, Kudi tabude yar pos din ta daniyar ta bawa mai mashin din , Amma sai Yusuf yabashi dubu daya nan mutumin yai ta zabga godiya, har zuwa lokacin da ya bude gaban motar tashiga, Sai a lokacin ta,ga Abubakar wanda ke barci a seat din baya, A hankali yafara tafiya duk da gaban ta yana mugun faduwa bata yarda yagane hakan ba don ta wani dake afili, Maryam yace acikin wani irin murya da ba,a,ta iya fassara shi ba, May yasa bakya ji ne wai for Allah sake may kike ji ga hawa mashin kina hada jiki da mazan wasu, Innalillahi ta iya furtawa don jin abinda yace Wani iska ya fesar daga bakin shi saboda haushin da yake ji ko zai samu relief, Yadan waigo inda take zaune a takure saboda sanyin A, C da ya fara ratsata, Yakara cewa I hate dis wallahi mace a saman mashin macen kuma wai,,,,,, Sai kuma yai shiru ya mai da hankalin shi ga titi, Maryam wace tun tana jin haushi da takaici zuwa yanzu abin mamaki ya koma bata, kawai, Sai ido ta samai yana ta masifa kamar wani mijin ta can A,A wanda yake tsaye bakin titi wajen wasu kanikawa ya hango su tafe a haka, Nan da nan wani irin gululun bakin ciki ya soke shi a zuciya, May guy din ga dan IBO ke nufi da shi ne wai, akan maryam, Don, dai ,something is fishing Jibrin ne yashigo garin yakira noban Yusuf yaji ko yana inane a lokacin, YUSUF ke cewa a cikin bacin rai gani zan shiga gidan sister, yanzu ok mu hadu a can Jibrin din yabashi ansa, Yana kashe waya yadan juyo inda maryam take zaune ciki dakewar fuska ya ce cikin sasauta murya, Maryam ke fa kikai min alkawarin bazaki kara hawa irin wanan mashin din ba, tsakani da Allah, Maryam saboda rudewa da yanayin da yai magana Tace Ya Yusuf dama kake son in fita da kafa tun daga gidan mu har Usubu gidan su Safiya,? Shiru yayi dan a lokacin baida ansar bata da zai mai sanyi a rai don haka kawai sai ya share da ita, A kofan gidan Anty suka samu su Jibrin din suna jiran shi, Hannu ta mika da niyar dauko yaron inda akayi dai,dai da shima yamika nashi don daukan, yaron, Kansu sne ya buge a lokaci guda ga kuma numfashin juna dasuke jin saukar shi tankar a hade suke sauke shi, Maryam ce tai saurin jaye jikin ta tabar mai yaron don ya hi, Yaron dake ta sharan barcin shi hankali akwance, Ta dan tka kadan Yusuf din Yace dakata ki shiga dashi pls, Cak tatsaya har zuwa lokacin da yakaraso zuwa inda take, Mikamata yaron ya yi inda suka kara hada numfashinsu fiye da wanda sukayi adazu cikin mota, Wani irin yarrrr taji wanda tunda take bata ta jin irin wanan yanayin ba, Ga kamshi mouth fresh din shi tana ji kamar a hancin ta, Sai kamshin turaen shi na THE da kaure ko ina ta juya agurin kamar yanzu ake fesa wa, A hankali ya sauke mata yaron a hannunta da ya hade da nashi kamar bai sani ba, Tajuya a hankali zuwa cikin gida da yaron rungumay a hannun ta kamar wace bata da lakka ajikin ta Saida yaga shigewan su sanan ya juyo inda Jibrin da sama ila suke a tsaye bakin motar su suna kallo drama n secret lover's, Gira Jibrin yadan daga mai cikin tsigar shakiyan ci Daure fuska Yusuf din yayi tankar bai fahinci may suke nufi ba, ZEEE. MAKAWA YELWA SEENABU 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI A hankali maryam ta mika hannu don daukan Abubakar wanda ke barci a bayan mota, Shima Yusuf a lokacin yakai hannun shi da niyar dauko yaron wanda ke ta barcin shi hankali kwance, Hakan yakawo masu sanadin musayan numfashin su a lokaci guda, Cikin sauri maryam tai yunkurin jayewa sai dai kuma ba bu filin da zata iya hakan, Shi Yusuf din ne bayan ya lumshi idin shi cikin jin wani irin yanayi na daban, Ya dauko yaron yafito dashi daga cikin motar mika mata yaron yai kokarin yi sai kuma hannun shi yadan kara,shigewa a na ta, Yarrr, taji tai saurin kokarin saita numfashin ta dake barazanan tsayawa, don shock, Nan ta dan wuce su jibrin dake kokarin fitowa daga cikin nasu motar shi da samaila, Anty Dije wace ke kitchen a lokacin taji motsin shigowar maryam gidan a lokacin kuma ga Abubakar a hannun ta, A nutse ta shimfide yaron wanda ke ta faman barcin shi hankali kwance kamar ko wani yaro, Da mamaki Anty ke kallon ta na ina suka hadu da ita . Ansa ta ba ta da cewa, a,saman hanya ina saman mashin muka hadu, dasu, Daga haka ta juya zuwa ciki inda ta kwabe hijabin jikin ta saman kujeran dake kusa da inda take tsaye ta aje shi, Wandon Jens din dake a jikin ta sai yar karamar rigar da tasa akai dai,dai iya kugun ta, ya tsaya mata , Shiyaba wandon ma,anan fito mata da surar jikin ta tsab waje, Mazaunan ta da suka dan baje a baya suka sa Sharp din fitowa fili da kyau, sai kuma kirjin ta da,surar su ya baiyyana tsab waje, Sam maryam ta shafa da cewa Yusuf yana a waje saboda hankalin ta na gurin da Anty ke girki, Dai tsakiyar gidan ta dan bar kofan shiga ciki ita kuma bata karasa kitchen ba Yusuf da Jibrin sukai sallama a cikin gidan, Sau guda yadan daga kan shi ya kallin wanan hallitan na maryam yai sauri kawar da kan shi yana mai cewa Barakallah masha Allah, Ta wutsiyar idon shi yadan saci kallan jibrin ko ya ga irin abinda yagani, Amma sai yaga shi jibrin hankalin shi na gurin Anty Dije wace suke ba,a da ita, Mamakin wanan irin girma da kyau da maryam tayi a lokaci guda yakeyi, Duk da ta ramay tadan yi wani faiyau da ita saboda yan maganganun dake ta tashi a kwanakin nan, Gaskiya wanda duk yakawo sa hijab Allah ya saka mai da,alheri saboda ba karamin abu ya boye wa mata ba, A hankali ya zauna yana mai lumshe idon shi tankar mai jin kasala, Duk hiran da Anty da Jibrin keyi yana jinsu idon shi a lumshe suke, Ya dan kai bayan shi a makarin kujerar da yake zaune akai, Hannun shi yasa yadan shafo fuskan shi da su round ya furzar da,iskan da ya kumshe a bakin a fili, Ismail ne ya kira jibrin din yana mai ce mai yazo mana su karasa gida ya shige ya manta da shi a waje kawai, Jibrin ya ce mai idan ka gajine kawuce mana kawai kada ka takuramin fa, Kasan ina tare da ogana ne, Sai a lokacin Yusuf yadan bude idon shi da suke a rufe tankar mai barci a lokacin, Yace kaje ka samay shi mana kada ya gaji da jiran ka, a waje, Jibrin ya ce kai ina bai isa ya hanani abinda nake son yi ba, pa, Katashi mu tafi 212 MOTOR, S ina son ina son in duba mota acan, Da mamaki Jibrin ya ke kallon shi yace Man duk motocin sa ka bari a Abuja sai a kwantagora zaka sai mota, Ansa Yusuf ya bashi a takaice da cewa basu da motocin kwaraine a gurin, Jibrin yace su na dasu mana lates one masu kyau kuwa, Sai bai kara cewa komai ba yai shiru kamar bashi yai magana yanzun ba, Ànty Dije ce tace kai amma ai maganar Jibrin gaskiya ne ko Yusuf kamar Abuja zai fi motoci manya ai, Hannun shi ya dake a saman goshin shi yacire a hankali, Saiga rinanun idanun shi sun fito waje jajir da su kamar mai ciwon kai, Yace cikin wani murya mai rauni Anty ki duba fa ki gani for Allah sake ai maryam ce nagani asaman mashi, again, Jibrin wanda ke kallon shi a cikin mamakin may zai sa ya nuna concern din shi haka akan wanan yarinyar karama, Anty ce ta tare shi da fadin ai indon hawan mashin ne duk shi muke hawa Yusuf, Shima baban Assalam naji yana cewa idan ya samu kudi zai yi kokari ya siyo mota ya ahe muna, Anty barin duba idan nasamu maikyau sai a saya ko anan din ne zai fi idan ma har zan aje maku driver ne kafin ku iya yadinga kai ku duk inda kuke so zaifi, Yusuf inji anty dije tace kayi hakkuri har zuwa gaba pls don mutane zasui ma zancen mumunar fassara akai, Kaga zasu ce ai don abin hannunka ne baba yake son baka mar,,,,,,,,, Sai tai shiru don tunawa da tayi cewa Jibrin yana gurin kuma shine wanda ya hada connection tsakin Yusuf da Sadiya, Tsab yamike tsaye yana cewa nifa anty ba ruwana da zancen mutane don ban zuwa gidan kowa tun farko sai nan, Fita yayi daga cikin falin batare da yai masu sallama ba ko yace wa jibrin su tafi, Anty taga kai takalli fafadan bayan shi har zuwa ficewar shi, Jibrin ya tambaye ta da hannu cikin alamar may ke faruwa, Ansa ta bahi da kafada ita ma batasani ba, gaskiya, Tun wanan lokacin Yusuf ya canza gaba daya bai daina zuwa ba amma baya wani walwala a gidan kamar farko, Don shi a ganin shi Anty bata sin abin hannun shi ne shi yasa ta doje wa zancen motan da koyaushe yake mata magana, Maryam yau da wuri ta gama duk wani aiki da zatayi don tana son yin kallon wani series film a wani tasha, Yaro ne mai zakin murya ya shigo gidan da sallama yana cewa wai ana sallama da maryam inji wani, Maryam wace ke zaune a kasan falon su saman wani dan filo, taji gaban ta ya fadi dam, Din tasancewa ba kowa bane A,A ne don shine mai wanan dabiar, kamar tace wa yaron bata nan sai dai ta daure ta ce kace tana tafe, Maryam tafito cikin shigar wani bakin dogon riga har kasa yana da kwaliya na wani pink colour, sai gyale kayan da ta dan yane fuskan ta dshi, Yana zaune cikin motarshi kafar shin guda ya daga waje, Fitowar maryam tun daga nesa yake sakar mata, murmushi, A zaton shi tunda har tafito wanan dan IBO barazanane kawai yai mashi, Ya masan cewa koda da gaskiya ne maryam bazatai wani wuyan shawo kai ba zata huce tayi hakkuri, Tun daga nesa yake kara kare mata kallon cikin so da kauna Yarinyar na burge shi tana bashi sha,awa uwa uba ga hakkuri, Irinta ce ya dace ya aje agida matsayin uwar ya, yan shi, Don zatayi hakkuri da duk wani kwaran nashi, a rayuwa, Barka da fitowa yace mata kalman da ya fara taron ta da,shi ke nan, Sai dai yau ansar da yasamu sabanin na kulllum ne, yaji, Lafiya dai ko malam tace mai cikin daure fuskan ta tankar bata san shi ba, Cike da mamaki yake kallon ta don jin tambayan da tai mai, Amma da yake dan duniya ne sai yai murmushi yace cikin kwarewa da zolaya, Haba sahibata fune duk akan tafiya ba sallama, ko may ye haka nan, ? Dan dakatawa yayi ya kalleta yayin da take a tsaye hannun a harde da juna saman kirjin ta, Maryam don Allah dai ki fahince ni sai kuma yadan dakata , Can ya dan kalle ta yace wallahia office din mu ne aka turani wani course na sati, a Lagos, Kuma zan makara idan nace sai nazo nan na fada maki , Zai ci gaba da tsarata maryam ta dakatar da shi da hannu cikin wani murya tace mai enough, Malam is over now bawai wani ya fada min ba ni da kaina na ganka Shima cikin murya makama da ta fada yace kina nfin karya zan maki ne ko may, Maryam tace mai cikin dakiya kamayi ai bawai wani ne yafada min ba, Kabani kunya wallahi duk yardan danayi dakai malam nake jin ka araina fiye da,duk wani da na miji, Bata karasa taji yace o wo, ke nan wanan dan iskan iyamurin ya hure maki kune,ko, Kin arda dashe sherin da ya kulla min ke nan akan ki, Dariya tayi tare da yar shewar bakin ciki tace dakata kaji Daga yau karka kara zuwa gurina kuma kayanka da ka kawo min ka aiko a karbar ma abinka, Indai nice mai yin aure to na fasa kaje gaba kasamu daidai da irin ka acan, Har zata tafi , sai kuma ta juyo tadan tako har inda yake, tace mai, kadaina, daukar alhakin kowa wallahi nida kaina ba na gan ka a gurin ba wani yafada min ba na ganka a kwanar kwangwara face to face da yariya a rungumay, Ido yafitar yafara borin kunya maryam juyawa tayi abin ta batare da ta tsaya jin abinda yake cewa ba, tashige gida abin ta zuciyar ta na mata kuna da wanan baki rana da ta gani, Kiris ya rage ta fashe a lokacin son irin yadda take ji a bin a ranta , Yakai wani wani lokaci gurin kamar wanda bai da kuzari bayan shegewar ta, A hankali ta iya furta Innalillahi wa inna ilaihin raji,un , Sai ta rintse idon ta gam tana mai jin radadin da take ji yana ragewa a hankali, Tagumi maryam tayi daga inda take zaune ta rasa, abinda yake mata dadi, Don dai iyakar cuta A,A ya cuce ta sai dai kawai Allah ya isan mata, Kai Allah ma ya isan mata din tunda bai kai ga nufin shi ba a gare ta, Muryam anty dije taji a bayan ta tana cewa tashi ki shiga ki kwanta, dare ya soma, Jiki a mace ta mike a hankali ta na dan dingisawa don kafarta yai mata nauyi , Saman katifa ta fa da faba dayan ta tare da sake wani irin kuka mai gumza, A tsorace Anty Dije wace ke dafa falo ta kwasan yara,zuwa cikjn daki, Karasowa tayi dakin da sauri inda take jin kukan kaunar na ta Marayam so kike ki kashe kan ki akan wanan dan iskan mutumin ko yaya, ? Jin kalaman Anty, ya sakata dakatar da kukan sai she,sheka takeyi, A gaban maryam din anty dije ta dawo ta tsaya inda take iya ganin fuskan ta, Abinka da dan uwa rabin jiki sai gashi ita ma Anty dijen kuka takeyi, cikin kukan take lalashin kaunar nata, Cikin tausayawa da nuna kulawa, take ta cewa ai bai kamata ki kuka ba maryam Wanda Allah ya hana ma A,A ya bashi Yusuf ai Alhamdullahi, ko ? Dagowa maryam tayi suka hada ido da juna ita da yar na ta, Sai kuma kawai tasa wani kuka, irin mai tsuma zuciya, Anty Dije hannayen ta duka biyu takama sai ta kai zaune tana mai watsawa yar uwan nata ido, Tace amma dai maryam kukan dadi kikeyi ko mai makon ki godewa Allah akan baiwar da yai maki da kuma wanda kike shirin riska, Shine zaki din ga butulce mashi haka kina wana kukan, A karshe dai bayan dogon nasihan da tasha sai ta sa hannun ta kamar karamar yarinya, cike da tausayawa tana cewa kiyi hakkuri haka kar kibari kowa yasan may kike ciki, Maryam wace kan ta kawai ta kada a lokacin don baza ta iya magana ba irin yadda take ji, gaba daya tasa ta rasa A,A ke nan har Abada, A haka anty ta samu maryam tai shiru, ta lafe tankar mai barci, Kofan ta ta rufo mata a hankali, tafita zuciyar ta fam da tausayin maryam,din, wace ke bukatar kulawa saboda rabuwa da,wanda ka saba dashi akwai zafi, Zaune su ke a falon gidan Yusuf din suna kallon wani plan din gina da akazana a wani farin takarda, Zanen Gida ne mai kyau na gani na fada suke kallo a takardan, Gaba dayan su, photo ginan ya burge su sosai duk sun mutu a kan shi, KB ne yace kai Man irin wanan gidan kawai mutum ya samu lafiyyan mace ya saka ta aciki, Kwashewa sukayi da dariya a lokaci guda gaba dayan su amma ban da Yusuf, Wanda yace kai KB kai baka da zance sai na mata, ko ba mace ai a mutum zai iya zama ahi kadai, Dariya suka kece mai dashi don jin abinda yace masu, Sai,da KB ya dan gyara zaman shi sanan ya ce wa sauran abokan hiran nashi, Wai ya zancen shi da Sadiya ce may ake ciki naji shiru mana, Yusuf da,sauri ya ce mai tunda kaji shiru ba,sai ka tafi ka tambaye taba ko may yasa kaji shiru har yanzu, Duk dariya suka kara sawa saboda irin yadda yayi mutum sam baya son ya zance mata, Jibrin ne ya ce kai KB nifa zancen sadiya din nan yasa mun rudani wallahi, Kamar ya ? Inji KB wanda ke dan kurban drinks a hankali daga cikin cup, Yusuf wanda yake a zaune idon shi na saman ties, kamar ba dashi a cikin hiran ba, Ya ba Jibrin ansa a gajjarce da cewa kaso rudewa ne Jibrin, Ni na fita cikin wanan zancen tun tuni ban ma son a tuna min akai, Kallon kallon suke wa junan su, sai mamakin cewa may yake nufi da fadar haka, Ya ce masu Yes now already ni har na samu wata wace, you all know her, Da mamakin jin wai sun san ko wace ce ganin da yayi suna mamakin maganar shi, Gyada masu kai yayi alamar eh tare da lumshe idon shi yana mai gyara zaman shin, Jibrin yana shirin magana ke nan Yusuf yatare shi da cewa ba kowa bace maryam ce kaunar Sister, Cikin mamaki wanan ya kalli wancan gaba dayan su sun rude da mamakin jin wai maryam, Yace yes insha Allah da ita hankalina yafi kwantawa sauran duk ba suyi min ba, Amma ita nasan tarbiyan ta da kuma halaiyar ta kaga abin zai zo min da sauki, Daga haka bai kara cewa kala ba ya ma juya ya basu baya, Ga magana a bakin su sai dai ba daman su yi ta saboda ba suga idon yin hakan ba, KB yace ya zatayi da mr lecturer din ta, ne don naga ta mutu ga son shi,ban san ta da kowa ba sai shi, Jibrin wanda ya ke kwance saman kujera yace kai wanan dama yan yan gidan su basu da mutunci Brother din shi ne fa yaiwa yarinyar nan ciki wani lokaci har muka je gurin shi, Yusuf yadan juyo gurin da jibrin yake zaune yace Ok, ok family din su guda ko Cikin tambaya, Nan ya kwashe yadda sukayi da shi last zuwa da ya yi su kai ta dariya, suna mai Allah waddai da halin shi, Da farko rayuwar jibrin yadan sosu da jin ansan da Yusuf ya bayar, Akan maganar cousin sister din shi sadiya wace har gobe zancen ta akan Yusuf ne,, Don haka jikin shi yaji duk ya mutu mai, tankar an aiko mai da mugun labari, sai kawai, Bai wani dade ba yace masu zai tafi sai yadawo, Yusuf wanda a lokacin duk hankalin shi yana akan wayar shi dayake tura sako, Fitan jibrin din gidan KB yace wa Yusuf mutumina fa bai ji dafin zancen ka ba, Kamar Yusuf din bai ji zancen shi ba sai kawai ya share shi,, Tafiya Jibrin ke yi a motar shi yana tunanen ya zasu kwashe da Sadiya idan har ta samu wanan labarin , Kodai ya kirata ne ya fada mata zai fi mai sauki Sai kuma wata zuciya tace mai kada ka fara shi ya zama hadin fitina idan kai haka, Kabarta kawai komin dadewa zata ji labari ai dole, Duk kwana biyun nan a takure maryam tayi su kamar a kurkuku, take Sam bata ko fitowa wahe tana daki a taure ba wani walwala a tare da ita, Nobar safiya ce yanuna kira a wayan ta a hankali ta mika hannu ta dauko wayan cikin wani irin murya mai kama da ta mai jiya ta ansa mata, Safiya din ce ta hauta da,sababi cewa yanzu ashe zaman su bana gaskiya bane tunda maganar ta ma sai dai taji shi gurin wasu, Maryam bata gane may safiya din take nufi da zancen ta ba, Sai take tambaya kamar ya wai, don ban fahince ki ba, Safiya tace ai gata nan zuwa gidan da kan ta idan tazo za tai mata bayani, Tana aje wayan takai kallon ta ga shimkafan dake acikin plate gaban ta kasa ci sai juya,shi takeyi da,spoon kawai, Anty dije wace ko kallo bata ishe ta ba saboda duk yadda ya kamata tai mata tayi amma,still taki sake jikin ta, Safiya ce ta shigo gidan tun daga nesa tagane cewa kawar nata na acikin yanayi don haka duk wani abin da ta nufi yi mata sai taji cewa bazata iya ba,, Sun gaisa da Anty Dije a cikin nuna kulawa da kuma tambayar ta mutanen gidan su, Safiya ta wuce zuwa dakin maryam don ganin maryam din ta tashi daga inda tske zaune zuwa ciki, Ido ta kura wa maryam din duk da ta bata tausayi amma sai ta dake ta ce mata wai may ye haka maryam baki da lafiya ne, ? Idon maryam da ya kawo hawaye take kokarin gogewa safiya din takai zaune tana mai kura mata ido, Safiya tace ina fatan duk wanan abin bawai don A, A kikeyin shi ba maryam, Shin maryam wai ke wace irin mutunce da bakya daukan kadara, ko shawara, Ana fa son musulmi da tawakkali a ko da yaushe idan abu har ya faru da shi, Sai a lokacin maryam ta dago idon ta da sukai lub, lub duk sun kumbure mata tankar ta yi jinya da dadewa, Tadan kalli safiya din tana cewa cikin yar murya may kuma kikaga nayi da zaki ce min haka, Baki safiya ta tabe tace idan har kina wanan haukar haka wallahi wata rana ke ce mai jin kunya , Shin maryam damay kikafi wanan bawan Allah ne wai,? Wallahi ina mai shawartan ki da ki daina wanan halin tun dare bai maki ba, Dubu naso ke Allah ya baki shine har kike butulce mashi, Kallon SAFIYA maryam tayi don jin da tayi tace wai dubu na,so, Suyi ta,so mana ni ina ruwa na kan su su ka,sani kaina na sani, Manzan Allah fa ya ce muna kada mu aminta da kafirai don basu kaunar har a cikin zuciyae su, Inna lillahi inji safiya Maryam kanki daya ne kuwa ? take tambayar maryam din cikin budan baki kalar na mamaki, Yusuf din ne kafiri kowa ye ? A takace cikin bacin rai maryam tace yan uwan shi dai, Wallahi safiya nayi ta ko,karin ganin na taushi zuciya na akan shi amma na kasa, Duk lokacin da natuna cewa wai da su zanyi taraiyya amatsayin yan uwan miji sai inji raina yana baci, Safiya yusuf furen kan juji ne,,,,,, ZEE MAKAWA YALWA [4/28, 5:33 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI _*Hakika fadin jin dadin yadda kuke min bazai yiwa da bazarku nike rawa tabbas na yarda masoyi masoyine kullum godiya gareku bata yankewa hakan yasa na baku wannan shafin dungurum gum masoya*_ ❤❤ ********************** ❤❤ Shiru suka yi gaba daya dakin kowa da irin abin da, yake sakawa a,zuciyar shi, Gama ga maryam wace ke sauke ajiyan zuciya akai akai Safiya ta kau da shirun da cewa ki tashi ki gyara jikin ki ki sake rayuwan ki tankar bake ce a haka ba, Sai a lokacin maryam tai dan murmushi jin abin da safiya tace , Abincin rana da Anty ta,gama ne ta aiko masu da shi a daki, Maryam tafito da kan ta ta daukan masu ruwan sha, a cikin fridge, Sun fara cin abinci ba da wani dadewa ba suka tsinkayo muryan Yusuf a falo, Anty Dije wace yan kan nen nata duk sun dagular mata lissafinta, Saboda sun tayar mata da hankali, shi Yusuf yana fushin a kan anty taki yarda,ya,sai masu mota, Ita ko maryam taurin kai kamar mutanen farko da basu yarda da sakonin su ba, Safiya ce taiwa maryam inkiya da cewa taje tai ma Yusuf sannu da zuwa, Ruwa yake kokarin tsiyayawa a cup don yasha, Maryam wace ta fito saye cikin dinkin buje da riga na wani material lace, ja colour mai yan fararen duwatsu, ajikin shi, Dinkin shi kamar maternity ya karbi jikin ta so sai yai mata kyau, Kusan kwanaki ke nan rabo da ya sata a idon shi tun ranan da suka dawo unguwa a tare, Cikin ladabi ta gaida shi ruwa ya ke tsiyayawa amma sai da mamakin gaisuwar da tai mai ya kama ta, A nutse ya karba mata don zaka ce ai ba shi ba ne take gayar wa, Sanin halin maryam da safiya tayi yasa ta fitowa ita ma daga dakin cikin fara,ar ta, Tana gashe shi da shigowa tana kuma kokarin samun gurin da zata zauna a daya daga cikin kujerun falon, Maryam wace duk a ta kure take saboda tana ganin cewa duk step din da tayi kamar a idon Yusuf yake, Kitchen ta nufa gurin da Anty ke kokarin shirya mai a bincin shi, Karban aikin tayi a hannun anty taci gaba da zuba mai, A falon su ukune zaune a ciki Yusuf kewa Anty Dije, bayani akan tafiyar mahaifin su kasa mai tsarki, Magana yake wa Anty dije a zahiri amma acikin zuciyar shi tunanen yakeyi maryam ce yake kallo a lokacin wace ke tafe , Ba komai yasa yake son yarinyar nan ba sai zaman ta irin macen da yake burin aure a rayuwar shi, Kunya natsuwa, kamun kai, rikon Addini tarbiya da kuma sanin darajan mutane, Itako maryam zancen da taji na tafiyan su baba shine ya ja hankalin ta, Badon komai ba sai saboda adduan mahaifin su ke nan a kullun shi dai yatafi makka ya gano kabarin Annabi da Abubakar da nana fatima, Duk addua sai kaji yasako wanan addu,an yau gashi Allah ya nufe shi da zuwa wanan shekaran, Allah sarki baba ashe Yusuf ne mutumin da,zai yi sanadin sauke faralin ka Tire din da ta dauko na abincin shi ta dire mai a gaban shi tare da kokarin jawo mai table din a gaban shi, Nagode maryam ya ce a takaice tare da cigaba da zancen shi, Wanan hali irin na godiyan Yusuf komai kamai kan,kantar abinda kai mai sai yayi ma godiya, Muryan maryam ce ya dakatar da shi daga bayanin da yake wa anty, ta A zuba ma ne ko ba yanzun zaka ci ba ta tanbaya cikin dukar da kai kasa, No, barshi kawai na gode ya ce yana mai daga mata hannu, Ta mike a hankali ta juya zuwa kitchen don ta rufo kofan da tabari a bude, Ido Yusuf ya kara binta da shi yana kara mata kallo azuciyar shi ya na,addua Allah yasa haduwar su ya, zama alheri a rayuwar su da haka yadan lumshe idon shi, Safiya wace ke gefe kuma tana nazarin duk halin da Yusuf din ke ciki ta dan murmusa daga gefe, batare da,sanin kowa ba, Maryam wace a lokacin tadawo cikin falon tana kokarin shigewa daki safiya ce ta dan jawo ta da fira, Tace maryam wayan nan naki ko yana yi yanzu ya daina hooking din da yake yi, Tafida hakan cikin rashin nuna wani abu a fuskanta, Sam mutum zai dauka cewa bada wani manufa tayi zancen, ba, Wanan maganar na safiya yadan sa maryam din dawo wa falon Gurin da safiya take a zaune ta nufa tana mai cewa cikinnmuryan nan na ta tankar ansa ta magana,dole ne, Kinsan yanzu kira kawai nakeyi da shi sai kuma received din called, kawai, Anty Dije ta mike a hankali tana cewa barin dan shiga cikin gida kafin ka gama yanzu zan dawo zan tura yaro can gidan mu gurin babane, Anty dije tana fita gidan sai Safiya tace au na fa manta da cewa za,a kirani nabar waya daki cikin sauri ta mike zuwa dakin, Tafiyan safiya yasa akabar su su biyu sai dan shiru ya ziyarci gurin abincin shi yake ci hankali kwance abinshi, Jin shiru ya dan ratsa gurin yasa lokaci guda Yusuf ya juyo yana fuskantar ta, Ba tare da yakalleta ba yana mai ci gaba da cin abincin shi yace, Maryam kwana biyu lafiya kike ko ? A bazata maryam taji maganar a lokacin hankalinta nagurin wayar ta da ke a hannun ta, A hankali tadago kanta sai taga cewa ai su kadai ne agurin kawai, Ko bakya magana ne kina tsoron kada na gudu dake tunda ba ki san koni waye ba ko, ? Ita dai maryam murmushi kawai ta dan sake wanda iyakar shi iya fuska, batare da tayi magana ba, Shima Yusuf di kamar yadda tai murmushin hakan ya yi nashi, Dukawa yayi yaci gaba da,cin abincin shi a hankali kamar yadda yake yi tun farko, Sai da ya kurba ruwa yadan jawo tissue yadan goge bakin shi , Sanan yace maryam nasan cewa kina mai jin zafin abinda A,A dinki yai maki , Maryam duk abinda babba zai hango yaro ba zai taba hango shi ba,. Don haka kibar wa Allah al,amarinki gare shi yafi duk wani tashin hankali da zaki saka kan ki a cikki, Ni har ga Allah idan zancen baba bai maki ba zan iya hakkuri da maganar Allah zai ban wata, Duk da nasan cewa nadade ina mai rokan Allah akan yaban mata daidai ni , Bako wani irin rayuwa nake bukata daga mace ba akwai wasu hallaiya danake son macen da zan aura ta kasance dasu, Sai ga shi ubangiji ya nufi baba da alkawaranta min Da na diba sainaga cewa aiduk wanan abin da nake bukata kina dasu har ma kin zarta wanda nake bukatan, Maryam kafin lokacin da baba zai bukaci jin hukuncin da muka yanke akai Idan har kinsan cewa bakya sona ko kuma kinada wani still wanda kike so , To ki fada min tun zancen baiyi nisa ba saboda ni mutum ne da bani son inwa babba karya ko yaudara, Dan shiru ne ya kara ziyartan gurin shiko Yusuf yana saurarenta ne ko za tai magana akan tambayar da yai mata, Amma sai yaga alamar baza tai magana ba ba zata ce wani abu ba sai wasa da wayan hannun ta da takeyi, Maryam yakara kiran sunan ta cikin wani yanayi da yasa ta rikicewa amma sai tadaure tana mai dago kai ta dan dube shi , Yanayin da tagani ga fuskanshi ba wasa aciki a lokacin don haka tai saurin dukar da kanta kasa tana sauraron shi, Ki daure ki fada min ra,ayinki a ganay dani amna dan girman Allah ina rokon ki da ki fada min gaskiyar abin dake zuciyar ki, Kada ki duba abinda ke tsakanin mu da baba ko Anty Dije, Saboda nayi alkawari bazan taba auren macen da bata so na ko wace bana ra,ayina ba, Ni mutum ne da bani da ra,ayin yin aure ,aure a rayuwa na, Don haka sai wace nasan cewa tana sona ina son ta zan aura bawai don ra,ayin wani ba can daban, Pls kada kuma kiji kunyar gaya min gaskiya don nasan ba dadi ka kalli mutun face to face kace mai baka ra,ayin shi, Amma ni agare ni gara hakan da ka yaudari mutun kafada mai karyan don kawai yaji dadi, Don haka maryam ina sauraren ki ki fada min ra,ayinki agamay dani pls ? Maryam wace kanta ke aduke lokacin a cikin zuciyar ta hakika maganganun uncle gaskiyane, Amma kuma taya zata fada mashi cewa yanzu ta amince dashi kai tsaye ya yarda da ita, Bayan yana sane da irin yadda akai ta kwasa da ita akan shi, Dakuma irin yadda son A,A ya ke azuciyar ta har bata iya boye, Tambayar ta ya karayi sai taga ai kawai tafada maigaskiya zai fi, Abin mamaki kuma sai taji bakinta yai nauyi ta furta mai ko wani irin kalma, Saidai kuma i zuwa yanzu karyane tace bataji wani abu akan Yusuf din ba , Saidai tana kokarin karyata haka din da takeji a kan shi tun bayan dogon sharhin da safiya ta zaunar da ita tai mata, Gashi kuma ya tsure ta da idon ta rasa yadda zatai magana har ta fada mai gaskiya,, Ganin baida niyar kauda idon shi gare ta dole ta daure ta ce ma wani abu saboda tasan yin shirun nata baida mafita, Kasa,kasa yaji muryan ta tana cewa kasan ai aure nufin Allah ne idan har Allah yakardara ni matar kace kamar yadda mahaifina ke bukata to,,,, sai kuma tai shiru batare da kara cewa komai ba, Murmushi Yusuf din yayi yadan gyara zaman shi yace Uhum maryam kifitar da duk wani kunya da shakku kiya magana don har yanzu banji kinyi maganar da nake son ji ba Tabbas maryam nasan aure nufin Allah ne, amma ni abin da nake son in ji shine Yusuf ina sonka ko kuma a, a yusuf bana sonka, Da sauri tadago kanta dake duke takalle shi shima din ita yake kallo sai yadan daga mata gira yace yes,haka din ne mana gaskiya, Hmmm kawai tace saine kuma tace, amma dai ai nayi maka bayani ko ? Tuna dai abin da kikace a baya kawai kince Aure nufin Allah kuma mahaifinki ke bukantan kiyi, Don haka kenan bake ke bukatan aurena ba har yanzu maganar mahaifinki ne kawai kike bi, Cikin sauri tadago kanta don jin abindayace tare da saurin cewa Injiwa ? Amsan da taba shiya dan sa shi dariya dan haka sai ya mike tsaye daga inda yake zaune, Gurin da take nufa kamar daga sama taji hannunshi acikin nata saikuma taga yakai tsugune agaban ta yace, Will you marry me ? ZEE MAKAWA YELWA,, [4/28, 5:35 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Barka da jumma,a yan uwa musulmai masoya novel din furen juji, Allah ubangiji ya karawa Annabi Mohammad, S,A,W daraja,👏👏👏 Jin hannun shi cikin nata, ya runtse, cikin nashi abinda bai taba faruwa da ita ba, ke nan, Aiko nan take jikin ta yafara rawa, don wani irin mugun tsoro ne ya shige ta alokacin, Shiko Yusuf yana ganin haka ya fahinci halin da take ciki hakan ya sanya shi kara rike hannun nata sosai, A hankali tadago idon ta da suka sauya zuwa na mai kuka, ta na mai wani irin kuka, Shima kallon nata yakeyi cikin cikin wani irin yanayi, Ido cikin ido kowa ke kallon dan uwa, wani irin kallo da kowa da abinda zuciyar shi ke fadi, Kallonta yake yi ita ma dai kallin nashi take tin cikin tuhuma da kaguwa ya sake ta, ba tare da sun daina ba, A hankali ya dago hannun zuwa bakin shi ya dan subban ta, Cikin wani irin sauri maryam tai kokarin jaye hannnun nata da yasha riko, Sai kallon kofa takeyi da alamar kada wani yazo ya riske su a hakan, ta ke wa gudu, Safiya ce tai murya tankar mai waya tana cewa hello, Ai ko nan take wani irin kunya ya lulube maryam irin kunyar da bata taba jin shi ba don gani take safiya ta ga halin da suke ciki, Cikin sauri da wani karfi ta fisge hannun ta yi masa wani irin kallo na don may, tai wani kasa da kan ta alokaci guda Ko shi Yusuf din sakin hannun ta yayi batare da bata lokaci ba don a zaton shi fitowa safiya zatayi a lokacin, Ya koma a kujerar da ya taso da farko ya dan kai bayan shi a kai ya kwanta, Ya na mai da numfashi da sauri da sauri kamar wanda yai wasan tsere, Jikin shi yaji yai mai wani irin sanyi gaba daya, don irin yanayin da ya riski kan shi alokacin da ya rikewa maryam hannu, A lokacin safiya ta kara so falon tawa maryam din wani irin kallo cikin wasa tace lalai ma maryam, May uncle ke fada maki haka da har kika mantacewa ina cikin daki tun dazu, Gashi har nagaji da jira ki na kai ga fitowa don ba gadin daki nazo maki ba, Kallon Yusuf din tayi wanda idon shi suke a lumshe tankar ba shi ba ne wanda ya dagulawa kawar ta lissafi har take ba tun kuka, Kallon shi tayi kamar ta yi mai magana sai kuma ta fasa kusa da maryam ta dan zauna,, Don ta kawar da shirun da sukayi a falon kowa da abinda zuciyar shi ke sakawa, Safiya, ce ke kokarin jan maryam da dan fira dan ta sake jiki, Maryam ta kasa cewa safiya din uffan sai da kai kawai take iya ansa mata, Ànty ce ta shigo dauke da wani ruba tab da wake mai ruwan milk a ciki, Maryam wace sai yanzu tai magana tun bayan halin da ta shiga, don haka har sadiya tagaji da fira da ita, Yusuf wanda ke zaune a gefe batare da yace wa kowan su komai ba , Sai tunanen zuci kawai yake yi, a cikin ranshi duk ya dabur ce, Tsam yamike yana mai yiwa Anty sai anjima jiki ba kwari, A lokacin da ya isa gidan shi zama yayi saman wani kujera, sai tunane kawai yake, Zuciyar shi tace mai Addu,a ce kawai ta kamance ka salim, Ka roki Allah shine kawai zai kawo ma ka mafita , Abinda zuciyar shi ta dinga raya mashi ke nan a lokacin, A take kuma ya amince da hakan, don haka da sauri ya mike zuwa bathroom din shi inda ya dauro alwala, Itako maryam bayan fitan shi suka hada ido da safiya sai kawai safiyan ta kwashe da dariya Wani dan filon kushin dake a gefen maryam ta dauka ta jefawa safiya din inda ta cabe shi a hannun ta, Tana ci gaba da yi,wa maryam, din dariya har da kyalkyatawa, Anty dije tagane may suke nufi amma sai kawai tashare su tankar ba ta fahince su ba, Don ta kauda zancen sai cewa tayi dan wake take son yi da wanan waken da aka bata gashi kuma milk colour ne zaifi kyau ga dahuwa, Sai a lokacin safiya tadan rage sautin dariyar ta tace wa anty aiko zai yi kyau so sai da dan wake , Har zuwa yamma Safiya na gidan sai a lokacin Jibrin yazo ya dauke ta ya mai da ita gidan su, A gogon dake false n gidan ya nuna goma saura na dare yanzu, Hakan ya ba wa Anty dije tabbacin cewa Yusuf ba zai shigo cin abincin dare ba ke nan yau, Don haka ta umurci maryam da cewa ta rufe masu gida don dare ya yi ko, Wanka tayi ta shirya cikin kayan barcin ta wando da riga masu ruwan light green, Ta daure kanta da ribon kamar kullun takawo gyale dan karami ta daure kan nata dashi, Zaune take bakin gadon su tana adduan shiga barci kamar yadda ta saba, Wayan tane yai kara a lokacin alamar kira ya shigo mata, Ta dan jima tana kallon wayan tana tunanen may zaice mata kuma yanzu, Har wayan na batun katsewa takai hannun ta tadauka tare da yin sallama cikin wata murya, Muryan wace ta sa Yusuf, kara rikicewa da jinta har ya rasa irin ansar sallamar da zai mata, Tunane ya farayi bayan ya karba wayan yana mai cewa, Shin wai dama haka wanan yarinyar take tun farko ko dai yanzu ne ta koma haka, Jin muryan ta tana gaishe shi yasa shi saurin tuna cewa a saman layi yake fa, Ansa gaisuwar na ta ya yi cikin wani muryan da zaka zaci ba ta shi bace, Shiru, ne yabiyo bayan gaisuwar amna sai Yusuf din yai kokarin kauda shirun nashi, Maryam ina abinci na ya tambaye ta cikin wani murya tankar ba tashi bace, Uncle abincin ka yana kitchen mana ko kazo ne mu bude gida, Sai da yai murmushin jin yadda ta rude a lokaci guda, Ya ce No na hutar da ke ni ina gidana ai, yau bana jin cin abinci sam, Kawai sai maryam ta tsinci kanta da tambayar shi ko saboda may ? Ya ce saboda ke maryam Yau kin sani a cikin wani yanayi kin ruda min zuciya ta kwata, kwata bani da sukuni yau, Maryam yadda tayi tankar Yusuf yana ganin ta a fili don nuna kan ta tayi tana tambayar ita,? Sai da yadan lumshe ido shi tankar maryam tana ganin shi, a fili itama, Yace Yes of course ke, maryam don kin sa duk na wani susuce akan ki, Idon ta tadan runtse saboda bakon ya,na yin da take ji a yau, Uncle din ya koma mata tankar wani bako wanda bata taba gani ba arayuwan ta, Daga haka yaci gaba da dan mata kalamai masu dadi a hiran nasu, Maryam wace sam ta kasa sakin jiki da shi sai ansawa da Eh Ko Um,umm takeyi sune kawai ansar nata da take iya bayar ba, Harzuwa dan wani lokaci sannan yai mata sallama, Sannu sannu ya dinga dan jan ta da hira tana dan sake jik wani lokaci tana hira dashi sama sama a kunyace, Wanan dan kwanakin da sukayi dan sabo maryam ta kara haddace ko waye Yusuf din, Tsab ta karanta halayan shi saboda shi mutum ne wanda keda wata irin baudadiyar ra,ayi, Idan har ba sanin halinshi kayi ba da wuya ka iya fahintar shi, Gashi miskili irin na karshe din nan gashi da saurin fushi, Abu dan kan kani zai bata mai rai amma kuma sai dai yana da saurin saukowa daga fushin Ga yin alheri a gurin shi tankar zuban habo daga hanci, Alherin shi irin ta bajintace, sai gurin da mabukaci na gaskiya yake yake yin ta, Abubuwa da dama maryam ta fahinta daga gare shi alokaci guda, Ko dan da farko bata damu da yanayin shi bane saboda kyamar da ta dora mai na gaira ba dalili, Tafiyan shi yazo kusa don haka ji yake yi tankar kada ya koma a wanan lokacin, Amma kuma yazama mashi dole yakoma din saboda harkokin shi da ke cen, Dama abinda ya kara tsayar da shi akan binciken da yakeyi a shagon mahaifin shi ne, Badon rai yaso ba yai sallama da su ya koma Abuja cikin jin wani iri, Sai bayan tafiyan shi ne Sadiya tasamu labarin cewa ai ya koma, Duk tasan cewa wanan zuwan da yayi kawai dai hakkuri tai ta yi don ba wani kulawa da ta samu daga gurin Yusuf din sosai, Jin shi shiru da tayine ya sa tabugowa wa Jibrin tana tambayar shi ko Yusuf din yana garin KG har yanzu, Amma sai kawai taji cewa wai ai Yusuf din ya koma, ko Sadiya wace wayar ya kusa sullubewa daga hannun ta saboda kaduwa, Hankalinta yai mumunar tashi ta kasa zaune ta kasa tsaye, Jibrin takara kira tana tambar shi ko may ya fahinta akan ta gurin Yusuf Bai boye mata komai ba ya fayyace mata a kan zancen, Wani irin mumunar faduwan gaba taji bayan taji cewa wai yasamu wata Sai yanzu tagane takuma fahici ko may yasa Yusuf duk zancen shi akan anty je ne, Idan ita kuma anty dijen ashe makircin da take kullawa ke nan, Don su mallakeshi su hada,shi da maryam din yarinya karama da ita, Gumi taji yana fito mata don jin wani irin zafin dake fitowa daga cikin ta, Ji takwyi tankar an watsa mata ruwane a lokacin Dije kinyi kuskure a rayuwar ki in har kina tunanen zaki iya rabani da Yusuf a lokaci guda, Dije sai na raba ku da yusuf sai na dasa tsana da gaba a tsakanin ku, Takai,wa hannunta guda naushi tana cewa daga yau zan fara yaki da duk wani wanda keda hannu acikin wanan maganar, ZEEE. MAKAWA YELWA [4/28, 5:36 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣6⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, YAURI *_Masoyan Yusuf da Maryam ku kwantar da hankalinku kar hawan ruwanku yatashi, abunda nikeso ku gane shine sadiyafa real lover ce_*😜 *_Koda yake naga ya'n yusmar team sun fi yawa amma kusani sadyus fa suma sun yunkuro sunce sune masoyan Yusuf na asali domin kuwa su ba hadin iyaye bane_*😍 ~*SADYUS team#*~ & ~*YUSMAR team#*~ 🤝 _Alherin Allah ya kasance atare da duk wani masoyin Annabin rahama_ 👏👏👏 😘all Sannu a hankali yake saukowa a matakalan jirgi, Saye yake cikin shiga irin ta,su ta mutanen kasar waje, Sai yar far glass da ya zauna mai a ido dagwas, kamar an auna shi, Daga inda ya ke ya hango shi yana saukowa a hankali, Murmushi yayi don ganin abokin nashi wanda yai mai tafiyan bazatan , Duk da sun dade basu ga junan su ba kowan su yaga dan uwa ya canza a lokaci guda, Hugging din juna su kayi,cikin farinciki da jin dadin ganin junan su, Surprise Sonny ya cewa Yusuf bayan yadan bubuga ma Yusuf din baya, Hannu rike da juna suka wuce gurin da ake ajiye motoci, Direct gidan Yusuf suka wuce inda suka samu taro daga kakan Yusuf din wace ke ta farin ciki da gani Sonny din, Sosai soni ya sake jiki ya kwashi girkin gargajiyan da aikai masu tsab ya zauna ya baje ya kwashi abin shi, Shima Yusuf yaji dadin wanan irin sake jikin da Sonny din ya yi, Wani tsadaden hotel aka kama ma Sonny din tare da yan rakiyan shi su uku, Sai bayan ya hutane ne Yusuf ya samay shi cikin shirin shi, Yana saye cikin jallabiya fara kal sai wata yar farar hulla da ya aa a kan shi , Hannu shi yana rike da wani dan farin tasbaha mai kyau yana ja a hankali, Sonny wanda a lokacin yana zaune yana game tare da wata yar zukakkan budurwa wace da gani yar kabila ce, Tun shigowar Yusuf din Sonny ya kalle shi saida yaji gaban shi ya fadi saboda irin yadda yaga Yusuf din ya mai wani irin kwarjini a ido, Zaka ce wani babban malami ne idan ka gan shi, Gurin zama Sonny din ya nuna ma Yusuf don ya zauna, Batare da ya kara ko da second a gurin ba ya juya zuwa wani dan karamin korido dake ta wajen dakin ya tsaya, Sonny wanda yagane komay Yusuf din ke nufi dole ya sallami yarinyar da suke zaune tare saboda yagane cewa saboda ita ne Yusuf bai karaso gurin ba, Sun kai wani lokaci, tare suna tataunawa akan har kan business din su, A nan Sonny yagane cewa Yusuf na, son karin taimako a harkokin shi don bunkasa har kokin shi, Bai wani ce ma Yusuf din komai ba a lokacin saboda shi kadai ya san may ya nufa a zuciyar shi, Washegari suka kama hanyan kauyen kakanin Sonny din, do halar ta bukin mutuwan kanin mahaifin Sonny din wanda yarage mai a matsayin dan uwa na kusa dashi, A zaton Sonny Yusuf bazai harar ci bukin ba amma sai yaga cewa dashi akai komai na bukin bine gawan mutumin, Bayan sun dawo Abuja da kwana biyu ne suka dan zagaya guraren masana,an tar Yusuf din tare da Sonny, Daga karshe cikin office din Sonny suka ka baje inda aka kawo masu dan abin ta bawa, Wayan Yusuf ce tai kara a lokacin, kamar kada ya daga amma sai kuma yakai hannun shi yasauki wayar, Maryam black, yagani a screen din baro, baro abinda yasa shi dan murmusawa ke nan, Yai mamaki matuka ganin Maryam ce takira shi, yau da kanta, Da sallama ya,dauki wayan yana mai dan furzar da iska abakin shi, Itace ta tare da fadin ina kwana bayan sallamar da Yusuf yai mata, Ahankali ya ansa a nashi bangaren yana mi lumshe ido don jin dadin muryan ta da yaji, A daidai lokacin Sonny yadago kai don ya tambaye shi a kan wani takarda dake rike a hannun shi, Ganin yanayin da Yusuf yake ciki yasa Sonny mamaki saboda bai taba ganin aminin nashi a cikin yanayin shauki ba, Don da gani ko ba,a fada ma ba kasan cewa ya fada tarkon soyayya ne, Muryan maryam ce ke cewa uncle Assalam ne yace a kira mashi kai ku gaisa, Murmushi yayi yadda har taji shi har cikin zuciyar ta, Wani irin abu taji ya daki, zuciyar ta a lokaci guda kamar an dan tsikare ta, Bata san lokacin da ta lumshe idon ta ba takai kwance daga inda take zaune bakin gado, Shima Assalam dake kusa da ita yana jiran ta bashi waya yai magana da uncle din shi, Binta yayi ya kwanta a gefen ta cikin kashe murya yaron ke fadin little mum bani wayan muyi magana pls, Dan harara takaiwa yaron don ya barta ta karasa wayan ta, tukun, Muryan Yusuf din ke ce mata, ke baki da magana dani ke nan ko sai Assalam ne zai ce ki kirani,? Cak taji numfashin ta yana kokarin daukewa don jin muryan Yusuf din datayi yana mata wani sauti a cikin kunuwan ta, Kara mirginawa tayi zuwa dayan bangaren gadon, gefe guda, Hello maryam bakya jina ne hlo, Shiru tayi tana yar dariya kasa,kasa tana wani dan lumshe idon ta, Ok tunda baki magana sai ki bani Assalam din shi dake son mu gaisa dashi sai mu gaisa, Ai bata san lokacin da ta mike daga zaune ba tana cewa Ai ina sauraron ka uncle kawai dai ban san may zance ba ne, Maganar ta yasa Yusuf dan juyawa da kujerar shi yana wani lumshe idon shi don jin dadi, Muryan shi cikin wani yanayi da sai ka saurara da kyau zaka gane may yake cewa, Da may kike cewa idan A,A ya bugo maki waya a lokacin, Wani irin juyi maryam tayi ta maida idon ta ta rutse su gam tana jin wani irin tukuki a zuciyar ta, a lokaci guda, Da uncle ya sani da bai kira mata sunan wanan mayaudarin ba a cikin wanan yanayi da take na shauki, Mikawa Assalam wayan tayi ta juya ta ba da baya tana mai fuskantar bangon dakin, Hira sukayi sosai da shi da Assalam din har yana kyalkyalawa dariya, Jin dariyan su da Assalam yasa har ta dan rage jin zafin da take ji da farko, Bayan Assalam sunyi sallama da Yusuf ne ya ce yabawa little mum waya din, A hankali yakira sunan ta bayan ta karbi wayan hannun Assalam din Jin Yusuf din ya kira, sunan ta cikin jan murya da kara harshe, Murya kasa, kasa yace i miss you maryam wani yarrr maryam ta kara cewa ta lumshe idon ta a hankali, Fuskan ta kumshe da murmushin jin dadi abin da ya ce mata, A zuciyar ta ko mamakin jin kalma da wai Yusuf ne ke fada wa ita maryam hakan, Anya kuwa ba wai kunnuwan tane ke mata karya ba, A hankali ta bude daradaran idon ta a hankali takai kallon ta ga kofan shigowa dakin su kamar mai kallo idan babu mai ganin ta ko jin may zata ce, Amma sai kuma taji bakin ta yai nauyi fada mai kwatankwacin kalman da ya fada mata, Jin da yayi cewa bazata ansa mai ba yashi cewa ok well ina aiki but anjima zan kira inji ansata, Da haka sukayi sallama da junan su yana mai mata bye, Yadago kai a hankali bayan yadan kawa wayan kallo kamar mai son ganin wani abu a cikin wayar, gami da sake wani irin lalausar murmushi, Caraf sukai ido biyu da Aminin nashi da ke zaune gefe yana mai wani, irin kallo cikin kurawa Yusuf din ido,, Duk da Yusuf din ya dan ji nauyi yadda abokin nashi ya ke kallon shi cikin mamaki, What's up ya cewa Sonny din cikin daga hannayen shi biyu da kafadan shi, Nothing's inji shi Sonny din ya mayar mai da martanin ansar shi kai tsaye, Duk kan su hankalin su ya koma gurin aiyukan da sukeyi ne, Kafin wani dan lokaci Yusuf din ya furza iska daga bakin shi alokaci guda kuma yai wata yar mika , Gabadaya Sonny ya dangware takardan dake a hannun shi ya dago kai cikin mamaki yana cewa, Whose is the lucky girl ? Yusuf batare da ya kalle shi ba ya cigaba da aikin dake a gaban shi, kawai, Har zuwa lokacin da Sonny din ya karaso gurin da yake zaune, A saman tebur ya zauna gaban Yusuf din, Ahankali ya sa hannun shi ya karbe takardan dake a hannun Yusuf din, Cikin zolaya yace ma Yusuf wanda yadago kai yana kallon Sonny din , Tell me how she look like,? Yusuf wanda yaso ya daure fuskan shi amma sai ya kasa saboda yadda Sonny ya tsure shi da ido, Dariya suka kyalkyala a lokaci guda gami da tafa hannayen su cikin na juna, Sonny yace ma Yusuf din, You are now in the team, Nan dai yadinga yiwa Yusuf din yan tambayoyi akan ko wacece wanan yariyar mai sa,a da har ta samu sace zuciyar wanan miskilin matashin maiji da kan shi a kan yan mata shekaru da dama, Sonny yace yana son yaga how beautiful she is, Yusuf yai murmushi yadan juya saman kujerar shi sanan ya tsaida idon shi ga Sonny din ya ce, She is not beautiful as you think, But she is very religious, Sonny ya ce cikin zolaya really, Kai kawai Yusuf ya daga mai alamar eh hakane, Dariya su kayi wa junan su suka tafa hannayen su a cikin jin dadin kasancewa tare da junan su, Wata guda,Sonny zai yi a cikin kasar shi kafin ya koma inda yafito yaje kuma zama, Sallahn Shafa,i da wutir ta gabatar daga inda ta idar da sallah ta ke zaune tana gyara jikin ta a hankali, tai shirin kwanciya barci, Ta mike a hankali zuwa gurin shimfidar yaran yayan nata ta gyara masu,kwanciyar su inda tabisu daya bayan daya kamar kullun ta tofa masu addu,oin shiga barci, AC dakin nasu tadan kunna masu don dakin yadan dauki sanyi kafin barci ya kwashe ta, Da Bissimillah ta hau gadon ta kwanta a hankali, Wani irin ajiyan zuciya tasaukar saboda sanyin da taji yana,shiga jikin ta, ga kuma wankan da tayi ta dinga jin tankar ancire mata wani nauyi ne ajikin ta, Idanun ta ta lumshe gami da jawo bargon ta har zuwa wuyan ta, Ga mamakin ta karar wayan ta ya shiga yi a cikin wanan daren, Da sauri ta mika hannun ta tadauko wayan da ke aje a side drower din gadon ta, Yusuf ne don haka tai mamaki jin kiranshi a cikin wanan dare don bai faye kiranta ba bayan goma na dare, Da wata karamar murya yakira sunan ta, amma sai tai shiru tankar bata a online din, Yasan cewa tana jin shi ansawa ne kawai aiki a gare ta, Wanda hakan na daya daga cikin abin dake kara burge Yusuf din akan maryam watau jan aji, Din haka yaci gaba da tambayar ta cikin muryan shi maikama da an tilasta mai yin magana, Kusan hiran hakkuri ya bata najin shi datayi shiru kwana biyu, Wanda aiki sukeyi sosai shi da Sonny dake kara mai fasaha akan harkokin business din shi, Cike da farin ciki maryam ke sauraren shi a lokacin amma bazata iya baiyana mai hakan ba a fili, A karshe yake sheda mata cewa Sonny zai shigo kwantagora saboda ya gan ta, Sai a lokacin Maryam tai magana cikin yar siririyar muryan ta tace ni ? Ni ? Da murya kamar wace zatai kuka a lokacin,, dama yasan haka zai faru don sanin halin ta da yayi, Jin shirun da yai yawa yasa shi cewa Maryam din dare yayi ta kwanta ta huta dama don yaji muryan ta da lafiyan ta yasa yakira ta Maryam wace taji dafin abin da yace tadan ji kunya ya dan lulubeta tankar ya gurin haka yasa ta kashe wayan cikin sauri ta koma saman filo ta kwanta rigingine tana tunane,, Shiko Yusuf din yamai da kanshi saman kujera yana mai lunshe idon shi cikin jin wani irin farin ciki, a rayuwan, A duk lokacin da yake waya da Maryam shikadai yasan irin yanauin da yakan shiga, Ya kasa fahintar ko may ye dalilin hakan kasancewa ai ba ita kadai bace mace ta farko da yake waya da ita, Amma sam bai jin wanan yanayi gurin sauran matan da yake waya da su, Maryam wace tun suna waya da Yusuf take jin alamar call na shigowa wayan ta, Amma ba dama ta diba don suna saman network ita da Yusuf, a lokacin badu jin ashhh,, Jin sako ya shigo yasa ta saurin daukar wayan da ta aje abayan filon ta, Azaton ta mutumin natane ya yo mata text din Nice, dream, Ga abinda tagani a rubuce kamar haka, Maryam kin bani mamaki sosai kuma na yardda cewa kudi suna iya canza mutum ko shi waye, Amma ki sani kinyi babban kuskure a rayuwan ki na zaban da IBO a matsayin gwanin ki, Duk da nasan badon Allah kike son shi ba saboda dukiyan shi kawai yarki makwadaciya ta saki son shi, Idon ta rintse don jin irin yadda ya aibanta mata yar uwa, Zaman ki ustaziya kamila ashe duk na iya baki ne baikai ciki ba, Idan har da gaske ke ustaziya ce ai abinda ki ka tsayar hujja akaina ba zai zama hujja ba, Sai dai ki min uzuri da nasiha akai har in daina dama ba sona kikeyi ba kindai yi amfani dani kin cin ma manufar ki kawai na haskaki gari an sanki, Idon ta takara rintsewa saboda jin wani irin abuda ya tokare mata zuciya, Bari kiji maryam da ace wanine zaki aura ba furen kan juji ba, Wanda daga karshe zaki fada cikin dangin arna ki haifa ma arna jikoki, Innallillahi wa,in na alaihim rajiun Abinda kawai Maryam take iya nanatawa ke nan don bazata iya karasa karantawa ba,, ZEEE MAKAWA YELWA Anty na Anty Nafisa harzami da maman Farida, Mariya SB Hafsat Yusuf, da duk wani masoyi na ina muna fatan alherin a rayuwan mu, Duk wanda ban ambaci sunan ta ba ina mai bata hakkuri dan Allah ,,, Nagode👏👏👏👏👏 [4/28, 5:37 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Barcin da gajinyan da take ji a lokaci guda tane mesu tarasa saboda wanin irin bacin rai da ya rufe mata zuciya, Shi A, A baiji kunyan fadar haka ba akan yar uwan ta, Sau nawa yana lalashin ta akan taimai hanya gurin Yusuf ko ta fada wa antyn ta akan a taimake shi Ya samu aiki a Abuja don yabar wanan lecturing din amma ita maryam din ke nuna mai cewa hakan ba daidai bane zubar da mutnci shine, Amma wai shine yau har zai kira ta da cewa makwadaita, Ita wani kwadai tayi da har za, ai mata wanan lakanin, Abinda take gudu ke nan tun farko,daya daga cikin abin da yasa, taki amincewa da zancen Yusuf din ke nan, Gashi tun duniya basu ji ba an fara mata gori akai wanda ita sam ba laifin ta bane, Hawaye ne masu dumi suka silalo mata daga cikin idon ta zuwa kumatun ta, Zaune take a bakin gado kafanta,zube a kasan gado Idon ta na kallon, kasan dakin kamar wace ke neman wani a bu a kasan gurin, Mikewa ta karayi tsaye zubur kamar wace aka tsikara, Hannunta takaiwa nashi da suke a dun kule guri guda, Ko mawa tayi guri da tashi tafada, da karfi saman gadon tana mai rintse idon ta, A hankali ta kai kwance daga gurin da take ta zaune idon ta a rufe Sai kuma hawaye suka fara malalowa daga idon nata, Daga har dare ya raba a hankali barci ya sace ta batare da ta sani ba, Anty dije ce ba taga maryam ba,a waje yau don haka ta leka, dakin nasu, A zaune ta hango ta ta kure guri guda, saman sallayan ta , Idon ta da taci kuka a cikin dare yayi sulu, sulu don kukan da taci da dare, "Maryam a cikin wani irin muryan, wanda ke nuna damuwa, Anty Dije ta kira sunan maryam din dashi, Inda tace haba maryam wai ke yaushe zaki fitar da damuwar zancen nan a zuciyar, ki ? Cikin idon da suka rine mata saboda wahalan da suka sha ga kuka ga rashin samun issashen barci, Tace Anty ni ban fa sa wani zancen damuwa a raina ba, Kawai dai fa irin zargin da mutane ke muna na akan wanan zancen, Murmushi Anty Dije tayi da taji abinda kaunar nata tafada Takai zaune bakin gadon su maryam din ta dan dago kai tanawa,maryam din kallo, Tace ni wallahi maryam duk abin da za,a ce bai dameni ba sam, Don Allah yasan zuciya cewa bana kwadan dukiyan Yusuf, Don ban taba rokon shi komai ba koda kuwa akan yadda zai tallafawa addinin shi ne, Maryam wace ke takure gefe guda ta sauke wani nau,yayan ajiyan zuciya a lokaci guda, Sai a lokacin maryam tai magana tace to amma ai mutane basu gani su, Don kinga kowa zargin ki yakeyi akai cewa kin sa dukiyan Yusuf a gaba kuma Badon Allah kike tare dashi ba,saboda abin hannun shine kawai, Murmushi mai daci Anty maryam tayi a lokacin saboda jin abin da yar uwar ta ce, Sai dai acikkin zuciyan ta, ta dauka cewa wani sabon fitina yar uwan nata ke son jawo kawai, Hannu maryam ta mika ta dauko wayan ta dake gefen ta, Dai, dai gurin text din da A,A ya turo mata cikin dare ta nunawa Anty Dijen Sai,da tagama karantawa tas sai tai wani dariya mai kama da yake, Tace to shine may maryam, har kike wahal da kan ki akai, ? Ai har fiye da,wanan sai ki ji a gurin mutane, balle shi A, A dake ganin cewa saboda dukiyan Yusuf ne kika ki shi, Maryam ta dago kai cikin kumburarun idanun ta tana kallon Anty dije da mamaki, Tace to anty shi,,,,,, Sai Anty Dije ta dakatar da ita daga abinda zata fadi ,, ta alamar daga mata hannun, Ganun haka yasa maryam yin shiru cikin ladabi tana mai dukar da kan ta kasa, Cikin murya mai kama da fada ko lalashi Anty ke magana, Ki kwantar da hankali ki duk abinda wani zai ce ki share mai shi hassada,ne kawai irin na dan Adam , In ba,shi ba da iyamuri musulmi da bayerabe da bature ke har balarabe idan ka aura sai anyi zuden ka, Saboda haka daga yau duk irin abinda wani zai fada ki dake ki shanye kiwa mahaifin ki biyayya kawai, Kai,kawai maryam ta gyada mata alamar ta gamsu da bayanin ta, Anty dije wace ke daga zaune tamike tsaye tana cewa maryam din ki tashi ki kama harkan gaban ki, Ki raba kan ki da tunane haka kada ki sawa kan, ki damuwar da har hawan jini zai kamaki a banza, Daga haka tabar dakin inda maryam tabi bayan ta da kallo harzuwa lokacin da ta fice, daga dakin,,, Zaune yake saman lalausar kujera guda daga cikin wa yan da ke cikin falon, Duk hankalin shi na ga Jibrin wanda ke bashi labarin irin yadda mutanen yankin kasar,, kwantagora ke da dawakai masu lafiya, Da kuma irin yadda matasan yankin ke wasan polo din su a cikin al,adun su, Da yadda,suke hawan Dabah a garin irin yadda matasa suke kara kawata abin gwanin ban sha,awa, Sonny wanda sai yanzu yadan gyara zama don yai magana yace very interests, How i wish to be there , Yusuf wanda tun fara hiran tsakanin Jibrin da Sonny bai ce kala ba, Sai yanzu yadan gyara zaman shi ya daina rubutun da yake yi a cikin system din shi, Yadago kai yace wa Sonny din ai sai ya gasu da, idon shi zaigane abin da shi Jibrin din ke nufin da kyau, Sonny wanda da farko yaso yai magana akai amma kuma sai ya ga cewan hakan, shi ya fi don yagani da idon shi,,, Sai dai kuma matsala guda ce a gurin shi ba komai ba, Saboda jin da,yayi cewa da mota zasuyi wanan doguwan tafiyan,, Shiko tafiya ko a cikin jirgi,ne bai son mai tsawo sosai, don baya son zama da yawa guri guda, Ga shi kuma, yana jin dadin labarin da Jibrin ke mai na al,adun mutanen kasan Kwantagora, Don haka yaji kawai zuciyar shi na bashi shawaran akan ya tafi yaganowa idon shi komai, Sai muryan shi suka ji kawai yana cewa When are we going there ? Ba Yusuf ba har Jibrin wanda ba wai ya san Sonny din bane da farko Sai da yai mamakin jin maganan da ya fito a bakin Sonny, Yadan daga masu gira irin na gogagun yan duniya yace Yes of,course i want to be there, Yusuf wanda ke sauraren su duk zancen da suke yi murmushi yayi kawai, Tun safe take, expecting din wayan shi, amma sai taji shiru, Tuna ne kiran shi takiyi amma kuma sai tana jin nauyin hakan Amma kuma maganar da Safiya tai mata akan tayi kokarin cusha kan ta gare ko da bata ra,ayin yin hakan, Don haka taji wani kwarin gwiwa yazo mata a lokaci guda, na takirashi, kawai, Bata lokaci tadauko wayan ta dake saman gadon ta, Dialing din nobar shi hannunta, yayi a lokaci guda taji kiran ya shiga, Har zuwa lokacin da kiran ya katse batare da an,daga wayan ba,, Tana kokarin aje wayan ne taji kira ya shigo a na ta wayan, Sai da tai wani dan murmushi irin da ke makalewa a can karkashin zuciya , Receiving ta dan,na bayan dan jan ajin da tayi bata dauka ba, Assalamu Alaikum ta fadi a cikin wani yanayin murya wanda zaka dauka yar larabawa ce , Sai da yadan rausaya kan shi daga gurin da yake kadan , sanan ya ansa mata, sallamar ta, Idanu a a runste tana jin wani abu na fisganta a zuciyar ta wanda bazata iya fassarawa ba, Muryan shi takara ji kamar mai mata rada a cikin kunen ta yana cewa, Hajiya maryam barka da warhaka, ya kuke ya yau ya su anty da Family ta ? Duk sai taji ta wani rude daga kawai jin muryan shi, da ta yi, Ya fahinci hakan daga inda yake don haka cikin lumshe ido shi, sai ya kawar da zancen da cewa,, Kin san kuwa cewa dama ke ce nake jira ki, kirani don in tabatar da zargin da nakeyi a kan ki, Sai dai kashhii, gaskiya zatona ashr ba gaskiya bane a kan ki, Muryan maryam cikin mamaki take tambayar shi ko wani zargine yake a kan ta, ? Cikin kashe murya tankar maryqm din tana agaban shi yace Ina Zargin Maryam, ce da rashin so na sai dai akan tursasawan mahaifin ta da yarta, A take taji wani irin nauyi da kuma kunya sun lulube ta saboda abinda yace, Zubewa tayi akan gadon ta sannan ta lumshe idon ta Bugawar ta zuciyar tana yi don haka tadan sa hannu tadafe gurin a hankali, Zuciyar nata kawai take iya sauraron bugawan nashi yadda yake karuwa Tambayar kan ta tayi may zatace mai daidai da ansar da ya dace da maganar shi ? Cikin wani irin murya taji bakin ta na ce mai amma ai ance zato zunubi ko ? Cikin yar dariya irin ta kasai,ta Yusuf yace kenan zaton ki nakeyi da hakan ? Yafada cikin wani irin murya kamar ba tashi ba saboda taushin ta, A cikin dabara maryam kau da zance don bata san may zatace a irin yadda take ji, ajikin ta, Ganin zata kawar da zancen yace a hankali cikin muryan nan nashi, Baki bani amsata ba maryam zaki kawo wani maganar ta daban, Murmushi tayi wanda har ya ji shi a cikin zuciyar shi, Wanda har saida ya lumshe idon shi don jin dadin hiran da su ke yi, Yace to shike nan tunda bazaki fada min ba amma fa ki sani dole sai kin ansa min tambaya na , Maryam wace ta sadad da kai kasa cikin jin kuyan tankar a fili suke hiran, Tambayar ta yakara yi da cewa "Kin amince ? Da cewa zaki bani ansar tambaya ta ko, Kai maryam ta daga gami da cewa "eh, tankar yana ganin ta , A cikin wani muryan farin ciki taji yadaki wani abu a gurin dayake , Ya ce "Great, maryam ko a haka na gamsu da ansar da zaki bani nan gaba, Nagode taji yace, Ba za ki taba regrets a kaina ba insha Allah, A zuciyar ta karba mai da cewa Ameen ya Allah, tana mai dan lumshe idanuwar ta, Muryan shi taji kamar a mafarki yana cewa Ina son ki maryam, Son da ban san lokacin da har haka ya shigeni ba a rayuwata,? Murmushi maryam tayi cikin jin kunya take cewa ai shi so ba sai an san lokacin shigar shi ba, Idanun shi yadan kara lumshewa yace Really ? Cikin alamar tambaya, Tagyda kai ta ce kwarai kuwa,, Cikin wani irin nishadi da jin dadi suka kasance tare a wayan har zuwa wani lokaci, Ganin lokaci yaja basu sani ba yasa shi cewa maryam har naji bana son ki ajewa yau, Dariya tayi mai sauti har saida yaji sh a ranshi yai mamaki kwarai yadda akayi yau tai hira dashi haka cikin sakin jiki Yau zuciyar shi ya tabbatar mai da cewa ya samu karbuwa agurin maryam, fiye da tsan manin shi,, Dan Allah kuyi managed da wanan nagaji sosai wallahi jiya nadawo daga gurin seminar,👏👏👏 [4/28, 5:38 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Zaune yake bayan sun gama waya hannun shi duk biyu a dukule saman habar shi, Tunane yakeyi na yadda yau maryam har ta sake jiki dashi suka dan dauki lokaci suna online, Gaskiya har zuwa yanzu zuciyar shi na bashi cewa akwai dai, Can kuma sai wata zuciya take tambayan shi a kan may zai damu da ko ma may ye, ma dai oho,, Don haka kawai sai ya ja wani dogon ajiyar zuciya ya furzar da iska daga bakin shi,,, Duk wanan abinda yake yi Sonny wanda yazo da niyar ti mai magana ya na tsaye daga kofan office din yana kallon shi, Karasowa yayi inda Yusuf din yake zaune yadan zagayo ta bayan shi, Sai da yadan dafa shi sanan yake cewa, Yusuf din, Ina mamaki irin yadda wanan Baby din ta samu sa,an ka haka, Idon shi yadan lumshe yai, rau da idanun shi cikin rausayawa, Ya ce, I really love the girl, Inji Yusuf yafada cikin lumshe idon shi, Sai kuma yai wani firgigit ya,dago kai yakali Sonny, ya ce, But she she is a small girl not More than 20 years now, What inji Sonny cikin wani irin mamaki ya tambayi Yusuf, Yusuf yadan gyda mai kai alamar abinda yaji ya fadi gaskiya, What a surprise, ? A small girl like dis charming your heart ? Sonny ya tambaya a cikin mamaki yace, kuma tasan yadda zatai handling din ka, Dariya kawai Yusuf yai mai ya mike tsaye daga inda yake Sai da yakai wurin window dake manne da office din yadan tsaya yana kallon motocin da ke sintiri a saman titin dake layin, Cikin wani irin murya mai amon wani sauti na fahinta yace, That is good characters in my religion, sai kuma ya juyo gurin da, Sonny yake tsaye yana kallon shi cikin mamaki, Har gaban shi ya karaso gab da shi har suna iya jin numfashin junar su, kamar zasu yi fada, Yace she is gift for me from Allah,,,, Naimat ce tashigo gidan Anty Dije da murnan su kowa ya tare, wanda hakan da akai mata yasa ta jin wani irin dadi a rayuwan ta, Maryam wace a lokacin tana, ciki bata san da zuwan Naimat gidan ba, Sai ganin Na,imat, ta tayi kawai gaban ta a tsakar gida, Itama dai da dan gudun ta ta tare ta suka rungumay junan su cikin jin dadin ganin juna Naimat din ce ta ture maryam din baya cikin batare tace wallahi maryam nayi fushi da ke, Kin sani sarai ni ka,daice a gidana Ibrahim baya gari amma ko ki kawo min ziyar haba maryam , banji dadin haka ba gaskiya, Cikin dan marai,raice murya maryam tace haba dai Naimat keep n fasan cewa ni kewa anty aiki yau she nake da time din fita, unguwa, Harara Naimat takai mata cikin wasa tace ke dai ba wani kawai dai ba ki so zuwa bane,, Dakin maryam din suga shige gaba dayan su a lokaci guda, Dan abin tabawa maryam takawo masu amma sai taga cewa Naimat, din bata ci komai daga cikin abinda ta aje mata a gaban ta, Don haka sai maryam take fadawa Anty cewa Naimat bataci komai daga abincin su ba, Bayan kamar yan mintina sai ga Ànty Dije ta shigo dakin Fuskanta dauke da fara,a ta samu guri kusa da Naimat din ta zauna, suna mai dan fuskantar junar su, Kallo guda Anty dije tai mata sai tai murmushi tace, May kike son cine Naimat, ? Naimat wace fuskanta ke dauke da murmushi ta dan dukar da kai cikin dan jin kunya ta ce , Anty ba ko,mai a barshi kawai , kamar ya za,a barshi haka zaki zauna da yunwa, A hankali tace inda zan samu shinkafa da wake da mai da yaji zanci, Inda maryam take anty ta kalla tace, muna da sauran wake ne , Maryam ta mike da niyar zuwa duba wake sai Naimat tace bani wayar ki maryam, Ba wani mussu maryam tamika mata wayan ta wuce abinta, zuwa kitchen, Ita ma Naimat din kwance takai ga wayan a hannun ta ta shiga gurare, Busy maryam take a cikin kitchen tana kokarin dafa abincin don kada Naimat ta matsu, Sako taji ya shigo a cikin wayan na maryam dake a hannun ta don haka sai tai kokarin zuwa diba sakon, A nan taci karo da sakon da A,A ya aikowa Maryam dashi, Tsab ta karanta sakon cikin tashin hakali da damuwa, Nobar Yusuf ta bida ta tura mai sakon , Sai kuma ta jawo nata wayan takirashi take sheda mai cewa itace ta tura mai sakon , Tagani ne acikin wayan maryam shine ta ce bari ta turo mai, Da sauri kuma tagoge kada maryam ta fahinci cewa, tayi amfani da wayan, Ba,a dauki wani lokaci ba da maryam tadawo dakin dauke da kulolin abinci a hannun ta, ta dire su a gaban Naimat, Sosai Naimat taci abincin don abincin yai mata dadi a baki, Ta dade rabon da taci wani abinci irin haka kamar yadda ta ci shimkafa da waken, Tana ci suna zuba hira da maryam kamar a bin hadin baki saiga, Safiya ta shigo gidan, Gaba dayan su suka sa ihun murna a lokaci guda , Maryam wace tasan da,zancen korafi a kanta a bakin safiya , Ta,sheko da guda ta,rugumay ta ta baya itama dai ture ta tayi tana cewa anya kuwa maryam idan kin yi aure zakiyi zumunci, kuwa? Bari har inyi auren kiga yadda zanyi ta zumunci da ku sai kun ce na i,she ku, A lokaci guda suka sa tsaki a tsakanin su don jin abinda maryam tace, Au to ku bari ku gani sai kun sha mamaki na tafada cikin tsigar zolaya, Safiyace bayan ta zauna take cewa tare da daga kai takalli maryam, A,A ya bugo maki waya ne maryam,? A lokaci guda fuskan Maryam ya sauya daga fara,a zuwa bakin ciki Batare da ta iya bada ansa ba tace, idon ta sun dan ciciko da hawaye kamar za su zubo, tace, Safiya pls kada ki kawo min zancen wanan mara mutuncin pls, Cikin mamaki suke kallon ta don jin cewa yau maryam ce da bakin ta take kiran A,A da wanan sunar, Safiya tadan gyara zama daga kan kushin din da take tace hmmm, Ji min ,fa A,A din nan dan wullakancin mutum kawai jiya yakirani da waya Yadinga surfa min zagi ta inda yake shiga ba nan yake fita ba, Wai mu makwadaita, macuta munyi mai butulci a kan kudi, Ba son Allah da Annabi kike mai ba tun farko don da,son gaskiya ne da baki canza ra,ayinki ba akan shi, Ke tun ina cewa ya tsaya in mai bayanin yadda zancen yake y Fam yaki yarda da zance na in fada maki har takai ni ma nafara mayar mai da bakaken maganganu, Naimat ce tace may ki,kacewa dan iska ke kuma,? Ta tambaya a cikin fushi da harshen hausan ta dake da surki da na kabila, Safiya tace haba ke ko nice fa, Har zaki tambayeni may nace mai, Ai saida ya shiga cewa kin gane ne safiya ki tsaya ki saurare ni ma wallahi,,, Tace kawai sai na kashe waya din ban son jin komai daga bakin dan iska kawai, Kawai ba,su ankara ba sai she,shekan kukan Maryam wace ke gefen su suka ji, Lokaci guda duk suka kai mata kallo a cikin mamaki, Da farko safiya tana zaton don tayi wa A,A cin mutunci maryam ke kuka, Amma sai suka ji muryan ta a cikin kuka tana cewa, Ban taba zaton cewa malam zai iya min irin wanan cin fuskan ba, Ida da har ina kwadayin dukiya ne ai da shine mutun na farko da zai fara shedan haka, Amma yafadi mana duk zamana dashi na taba rokon shi ya bani koda kwandala ne,, Nan dai suka shiga bata mussalai, masu ma,ana har ta dan kwantar da hankalin ta,,,, Zaune yake saman kujera yana karanta text din sai kawai yaji cewa bazai iya karasawa,ba, Don haka ya aje wayan saman table din glass din da ke a gaban shi cikin bacin rai, Wani irin abu yake ji a zuciyar shi takar idon shi zai rufe, alokacin, Ji Yusuf yi bai ma san may ya ke ciki ba a lokacin, Don haka sai ya ji tankar numfashin shi yana shirin daukewa a lokacin, Da kyar ya iya nemo natsuwa ya ya furta a hankali yayin da yake dafe da kan shi dake mai ciwo tankar ya tsage, Yace, Innalillahi Wa, Inna, Ilaihim, Raji,un Ya jima shiru dafe da hoshin shi da hannun shi guda a hakan yana nanata wanan addu,an, Sannu a hankalo yadan dinga jin zuciyar shi na walwalewa a hankali daga kuncin da yake a ciki da farko, Mikewa yayi zuwa bakin window falon shi,,yadan furzar da iskan kamar yadda yake yi, idan yana cikin yanayi, A,A ya ambata a hankali insha Allah zan gwada, maka cewa wani dan furen jujin yafi dan furen gida mutunci, Zan gwada maka cewa imani da biyayya suna da amfani ga dam adam , Daga haka yaji wani irin tukuki ya taso mai don haka bai iya cewa komai sai kalman innalillahi da yake ta nanatawa a cikin ranshi, A hankali ya tako zuwa dakin shi yana mai tunan cewa lalai A, A zan gwada maka cewa, Ni Yusuf nagaji sunan kwarai da ga mai sunan ,, ni Namijin Gwarozo ne acikin mazaje, Ba dan akuya ma ciyi amanan diyan mutane da abokan azarki ba, Daga haka yaja kafar shi da kyat har ya isa bedroom din shi,, A rigingine yakwanta yadinga tasbihi ga Allah ubangijin shi, tare da neman a fuwan shi, Yasan cewa wanan irin gorin shigar shi cikin addinin, musulunci da mutane ke masa, Ya ringa yin addua akan Allah ya bashi ikon cin wanan jerabawan da ya ke acikin sa, daga kuma neman rinjaye akan masifun da yake fuskanta, A haka ya dinga juyi a kan gadon shi yana tuna irin kalaman da ya ke fuskanta daga mutane da dama akan musuluntar shi, Jikin shi yana jin shi tankar anyi mai duka idon shi sun kada sunyi jajir, rayuwa gaba daya yafita ran shi, Allah gafurur Rahimun, yana, nan cikin wanan halin, ne barcci ya dauko shi, Ya jima sosai yana barcin bai farka ba har zuwa lokacin da nauran da ya saita masu tayar dashi daidai lokacin sallah, Tabbas yaji dadin wanan baccin da ya samu yayi ,, don yaji saukin Don da bai yi barcin nan na a haka zai wuni cikin bakin ciki da kunci,, Wanka ya fada yana fitowa ya wuce massallaci, Bayan yadawo ne yaji shi wani wasai da shi duk wani bakin ciki da kuncin da yake, ji ya daina jin su,gaba daya, Dining table ya nufa inda yasamu hamza ya hada mai abincin shi, haka ya dinga cusawa a cikin shi, har sai da yaji yayi dam, Komawa yayi saman two sitter yadan kwanta kamar mai yin barcci, hannun shi rike da goshin shi, Tunane yake yi don sai yanzu yasan ko may ye so, Tabbas bai taba sanin cewa ana son mutum irin yadda yake jin Maryam a,rayuwar shi a halin yanzu, Kusan kwana biyu yana cikin wanan damuwar idan kaga walwalar Yusuf sai idan yana tare da,Sonny ko Jibrin Lokacin da Sonny ya gama abinda yakeyi a garin su, Don haka sai suka fara shirin tafiya kwantagora ganin kayan al,adu kamar yadda,Sonny din yaji labarin su daga bakin Jibrin abokin hiran shi da yawo, Shiri na sosai sukayi saboda irin shigar da zasuyi yana bukatan kudade, da sauran abubuwa, Ba su wani dade a hanya ba ko da suka taso, Saboda irin gudun da sukeyi ga kuma motocin su lafiyyayu ne so sai, Sun iso lafiya garin sai dai wanan karon bai wuce direct gida Anty nashi ba, Sosai tun a hanya Yusuf ke kallon tsarin kasan hausaw yana mai yabawa da irin abin da yake gani, Shigowan su garin yakara sa Sonny rudewa sosai don gani yadda garin ya tsaru tsab, Yusuf ne ya dan sulale zuwa gidan Anty nashi don ya sanar masu da zuwan Sonny, Ya iso kofan gidan su Anty Dije din inda yaga samarin dake fira kamar kullun Sun mike sukayo kan shi cikin murna danuna jin dafin zuwan shi,, Wanda hakan ba karamin dadi yaiwa Yusuf din ba, a cikin ran shi, Don ko ba komai sun nana mai kulawan su gare shi, Nan suka,shiga jiddan kayan tsaraba zuwa cikk cikin jin dadi, Anty Dije ce ya riske a kofan kitchen tana kokarin dauko plate a mazaunin shi, Tana ganin Yusuf da jin sallamar shi ta mike da fara,an ta tana mai sannu da zuwa da bakin da babu sanarwa, Ya yai dariya duk da yau kawai sai ya tsinci kan shi da jin kunya da nauyin anty din, Yakaraso gaban ta yadan rusunna, yace Anty barka da gida, Cikin dan hararan wasa tace gaskiya Yusuf kana son muyi fada yanzu, Dariya yakara yace tuba nake Anty na tafiyan bazata yazo min, Shiru Anty tayi cike da mamaki, jin abinda yace batare da taga wani alamar waaa a fuskan shi ba, Sai kuma batayi magana ba tace to sannun ku da zuwa, Ya amsa da cewa yauwa Anty mun samay ku lafiya, Sai dan satan kallon ko ina yakeyi ko zai hango maryam da idon shi, Ya dan fuskan ci anty din yace wanan karon fa sa bako nazo anty, Gaba daya hankalinta ta mayar gareshi don jin abinda yace, Falin suka shiga a lokacin,sanan yakara cewa wa qn a bokin nawa dake South Korea shine mukazo dashi don yaga gari, Zama yayi yana mata bayanin makasudin zuwan Sonny kwantagora, Maryam wace kamshin Yusuf kawai ya isar mata isowar shi gidan daga gurin da ta idar da,sallah ta kwanta, Zubur tamike daga saman abin sallah da take kwance tafito daga dan wajen window inda zata ita hango Yusuf din, Daga inda take tadan daga labule tana hangen shi, Yana saye cikin wasu kanan kaya da suka kara mai kyau suka fitar mai da kurciyar shi da,wayewar shi fili, Hannayen shi suna zube a cikin aljihun wandon, shi, Wani irin lumshe idon ta tayi lokacin da hancin ta ya shakan mata kamshin shi, Jikin shi ne yabashi cewa ana kallon shi don haka yadaga ifon shi, zuwa kallon gurin da take, Daidai lokacin da ta bude lumsasun idanun ta suka hada ido da Yusuf din, Cikin sauri maryam din ta sake labulen tayo baya tana mai dafe kirjin ta tankar wace taji tsoro ko taga abin tsoro, Wani irin lalausar Murmushi ya sake a lokaci guda, Son Maryam din ne yaji yakara shigan shi a lokaci guda,, bai taba jin yana son mace haka ba sai wanan karon, Muryan Ànty ce ya katse show din itace ke kiran maryam din, Sai da ta sa wani dan karamin hijabin ta baki a saman kayan dake a jikin ta sannan tafito cikin tako guda guda, Kanta a kasa ta karaso gaban su saboda kunya, duk ya rufe ta, A hankali tace mai sannu da zuwa uncle ya hanya,? Tafadi a hankali kamar wace bakin ta ke ciwon magana cikin wani irin taushin murya, Daga Yusuf har anty yanayin maryam ya basu tausayi , sai dai duk suka share, Ta juya zata wuce ne anty tace cikin murya maikama da rauni, Tsaya mana maryan ku gasi zan dan shiga gidan lami in samo kankara ne, Bayan wucewan anty ne makwabta Yusuf wanda ke zaune dan nesa kadan daga gurin da take tsaye kamar kwance saman bayan kujera, Kanshi yadago yadan kalle ta cikin wani irin yanayi mai rikitar wa, Da sauri maryam takara dukar da kanta kasa tana wasa da yan yatsun ta, Batayi aune ba sai ganin mutum tayi a gaban ta tsaye yana mata wani shu,umin murmushi, Murya kasa kasa yace baki yi murna da gani na ba ke nan ko ? Jin hakan yadan sata saurin dago kai suka kara yin ido biyu karo na biyu da shigowan shi, Ido ya kashe mata wanda hakan yasa maryam din duk ta wani rude a lokaci guda, ta dago idon ta cikin rudewa da razanar Nan da nan gangan jikinta yadauki rawa don jin numfashin Yusuf din gab da ita, Ganin irin yadda maryam din ta rude a lokaci guda yasa shi tsayawa yana mata wani irin kallo cikj. So da kauna, Ji yake a lokacin tamkar ya rungumay maryam din da gagawa, Amma yin hakan haramun hakan bazai yiyu a garesu ba, Dole ya tillasta kan shi da dan ja da baya daga kusan tan junan da sukayi suna fuskan tar junan su, Maryam yakira sunan ta cikin wani kasalalen murya tankar wanda ya tashi daga barci, Yace may yasa kika ki bugo min waya tun daga wancan ranan da kika kirani,? Idan kuma nakira baki picking, Why maryam,? why ?, Yafada tankar wanda zaiyi kuka alokacin don wani irin abu da yaji yana fusgan shi, Tabbas komai yana iya faruwa a irin yadda yake ji akan ta Da gagawa ya juya zuwa gurin da yatashi da farko ya zauna, Lemon da Anty Dije ta aje mai saman table ya tsiya a cup, Sai lokacin maryam tadan saita kanta daga ruduwar da Yusuf yasakata a ciki cikin yan dakikoki, Muryan shi taji yana cew ina da bako maryam, Ina son ki shirya muje ki gaida shi, Da sauri tadago kan ta takaima gurin da yake kallo, Kai ya gyda mata yace yes zuwa gobe zan zo in dauke ku keda,su Assalam mutafi, Sai alokacin maryam tai wani irin ajiyar zuciya har Yusuf din yaji ta daga inda yake, Kallon ta yakara yi kawai cikin wani shu,umin murmushi sai kuma ya mike tsaye batare da yakara kallon ta ba saboda ba zai iya jurewa ba a irin yadda yake ji, Don maryam din yaga takara mai wani kyau da girma ga kuma haske da tadan kara, akan bakin tada ke shining, Daidai zaifitane yace sai ki shirya zuwa gobe din zan kiraki in fada maki time,,,,,,,, ZEEE MAKAWA YALWA [4/28, 5:38 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 7⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Anty Saffena, Anty Nafessa harzami, Anty Hafsat Yusuf, Maman Farida, Anty Bintu katsina, Maman Walid, lovely Daughter na Jamila Safiyanu, Tare da duk wacce ban samu ambatar sunan ta ba aciki da fatan zaku yafe min rashin sa sunan ku a jerin sunayen da nazano,, Allah ubangiji yakara dauka da bude da rahamansa agare mu baki daya, nagode kwarai yan uwa da irin kulawar da kuke bani a kullun tare da fatan zaku dinga hakkuri dani a koda yaushe, 👏👏👏👏👏👏👏 Saye take cikin,wani dogon riga, mai ruwan Jan colour,,, duwatsun jikin rigar ,farare, ne, Dinkin dogon hannu ke a jikin rigar , Sai gyalen rigar tadan yi roling din kanta dashi, Sai yar karaman, jaka fara da ta rika a hannun ta, shima yana da wasu stones farare, Assalam da Issalam suna sanye cikin shigar English wear, masu kyau da daukan ido, Safiya ma tana saye cikin wani dogon riga light, green, mai kyau dinki shi kamar ta banga, rigar ya karbe ta, Wanan karon Jibrin ne ya zo da su, daga gidan Anty Dije zuwa gidan Yusuf inda su kaiwa Sonny masauki, Abincin lunching ne suka dauko daga gurin big Anty din nasu, Waje suke zazaune saman fararen kujeran roba, suna shan iska, shi da Sonny, Motar da ta stsaya daga dan nesa dasu kadan hankalin su ya kai garesu, A hankali suka sako kafan su daga wajen motar, kafan maryam dake saye cikin wasu fararen takalma masu wasu belts a bayan su, Sonny wanda hankalin shi na gurin motan don ganin cewa a kwai mata a cikin motar shiko dama mayen matane,, Maryam wace kafar ta kawai ke a waje, ita bata fito ba tukun, Yaran ne suka fito da murnan su don hango uncle da sukayi zaune daga nesa saboda basu san cewa yazo garin ba, Sai safiya ce tafito a gaban motar tare da Jibrin din, Yusuf wanda ke rugumay da yaran ajikin shi yana masu magana hankalin shi ya koma gurin da ya hango ta fitowa daga cikin motar,, A hankali tafito daga cikin motar yayin da take dan gyara rigan ta a hankali, Daidai lokacin Safiya ta zagayo ta iso gurin da maryam din take tsaye, Sonny dake masu kallon kurulla kamar yana son ya, ga,no munin mutum daya daga cikin su,. Tafiya sukeyi jikin su na wani rausayawa kamar kifi,, Sonnu wanda numfashin shi yai kamar zai dauke saboda ganin wa yan, nan zukakkan yan matan dake tafe in suke, Kuma wai duk a cikin wanan garin da yake ma daukan kauye a idon shi, Wani irin kyaune ga wanan yariyar dake baya saye da Jan riga haka,? A cikin wanan takon nasu na natsuwa har suka karaso inda su ke zaune, Idon Sonny din har zuwa lokacin da suka karaso gurin nasu kyam a kan su, Maryam wace wanan kallon da yake masu duk ya takura ta ji take kamar ta shake shi, Kujeru suka basu suka nuna masu gurin zama inda Yusuf din yai masu nuni da su zauna, Ko zaman a cikin natsuwa sukayi shi tare da nuna kamilanci a tare da su, Sai a lokacin da, Yusuf yaga sun zauna ya dan waigo da hankalishi gaba daya gurin su, Yana masu sannu da zuwa a cikin harshe hausa, Sai a lokacin ya waigo gefen gurin da Sonny din yake zaune tankar ruwa yaci shi, Muryan Yusuf ne yaji yana cewa Mr Sonny meet , Maryam and Safiya our fiance, Firgigit ya farko daga tunanen da yafara yi naganin yana holewa da wa yan nan kyawawan yan matan , Hannu ya mika wa maryam da niyar wai su gaisa, Kai maryam ta gyada mai, alamar a,a cikin wani shu,umin murmushi amma acikin rata sai kiran Wa,iyazu billah, takeyi, Subbahanallah lokacin da sautin muryan ta cikin wani irin murya ke cewa is forbidden in our religion, Amma sai ta daga mai hannayen ta biyu ta hade su guri guda alamar gaisuwan musulmai, Ba Sonny din ba har, Yusuf da Jibrin ma sun mato a sauraron shi, Wow, yace I like your style girls, Ai fa tuni maryam ta tafi da imanin Yusuf din wanda yake jin tankar a yau yafara ganin maryam din tashi, Ga kuma wani abin bajinta da tayi a gaban shi yanzu wanda yakara sa shi jin ta a ran shi, Duk yadda ta ga,suna girmama Sonny da mutunta shi bai sa tayi gigin bashi hannu ba, Kamar irin yadda wasu wayayyu keyi wai saboda waye wa ko boko, A gaskiya duk yadda zai yi insha Allah dole sai ya mallaki wanan yarinyar a rayunwar shi, Nan ya shiga gabatar mashi da su da yaran da kuma bashi dan labari akan yaron shi a bokin shi Assalam, Maryam ce tadan diba agogon wayan ta sai tadago kai ta dan kalli gurin da Yusuf yake zaune rungumay da Assalam Alamar zasu tafi taimai da kai inda take nuna mai time cikin hikima, Wani lalausar murmushi ya sakar mata saboda tun dazu yagane cewa a takure take zaune saboda , Irin mugun kallon da Sonny ke mata, daga inda yake zaune,, Yusuf din ne ya mike tsaye daga inda yake yana cewa Jibrin ka mai da su gida saboda time din sallah ya kusa, Ganin Yusuf din ya mike suma suka mike tare a lokaci guda suna mai yiwa Sonny din sallama, Dakatar da su yayi ya shiga daga cikin gidan dan jim kadan yafito hannun shi dauke da wasu ledoji masu a lamar,tambarin shago a hannun shi, Ledan dake dauke da tambarin, kamar na yan kwallo, Ya,mikawa, maryam, sai kuma Safiya, da ya mikawa gudan, Thanks, suka ce mai a lokaci guda yayin da kowace tadaga ledan suna mai gwadawa Yusuf din da Jibrin, Yar dariyan yake yi maikama da yake, a fuskan shi, Amma shi yusuf a ran shi jiyakeyi tankar ya shake Sonny din saboda irin manyatacen kallon da yaga yanawa maryam din, Shiko Sonny wanda ya kashe su da ido sai mamakin wanan sarauniyar kyau da yagani a gaban shi, Kamar yadda Jibrin yazo da su da farko hakama wanan karon shi da kan shi ya mayar da,su gida, Shigar su gida yai daidai da shigowan kira a wayan ta, Ko bata diba ba tasan cewa Yusuf ne, Maryam, tayi yar murmushi, tadiba tana mai lumshe ido, Don haka batare da ta tsaya gurin Anty Dije kamar yadda tai niyya ba, Ledan tsaraban kawai ta aje mata a gaban ta, ta shige dakin su, Itako safiya dama tana kofar gida bata karkare shigowa ba sun dan tsaya da Jibrin din ta a waje, Maryam tana shiga daki tai receiving din kiran tana mai kara wayan a kunnen ta Tana mai cewa Assalamu Alaikum, wani iri yaji a kunen shi yarrr a lokacin da sallamar ta yadaki kunnen shi din Murmushi yayi yana tambayar ta da cewa sun isa gida lafiya ko, Ta ansa mai da cewa lafiya kalau har ta shigo ciki ai, Dariya yayi yana cewa ai yasan ko minti nawa ne zai kai,su gidan dama, Sai kuma taji a lokaci guda yai tsuki, ya wani ja wani, irin numfashi, Cikin sanyi jiki murya maryam ke tambayan shi ? My ya samay ka uncle, kuma,? Ya saki wani ajiyan zuciya yace, Kyale ni kawai maryam nayi da na sanin zuwan ku gaida wanan dan iskan wallahi, Mutum kamar maye kadinga kallin matan mutane haka,agaban ma,ajen su ,, Baki ji yadda kirjina yake min zafi ba wallahi inda badon bako na bane da ba,abin da zai hana in dake shi yau, Sakin ajiya zuciya maryam din tayi ta lumshe idon ta, Tace kasan wanda baida tauhidi bai dauki irin wanan abin a matsayin sabon Allah ba, Tace amma sai naga kamar mun fi shi laifi ai muda muka tafi hakana gurin shi batare da mun sa zumbudeden hijabi ba Yusuf daga inda yake ya lumshe idon shi saboda jin abinda maryam din tace don tabbas gaskiyar maganar ke nan, Wani irin kishin abinda Sonny din yayi dazu ya baibaye mai zuciyar shi, Sai da kyat yai kokarin kwantar da zuciyar shi, saboda kasancewa Sonny bakon shi, ne, A haka sukayi sallama da maryam din yana mata godiya akan irin yadda suka yi da bakon nashi,,, Bayan sallamar su yai zaune yana mai kallon wayan nashi tankar maryam din ce a gaban shi a lokacin Sai kuma ya juya tunanen irin hali rayuwa na maryam, Abinda yafi burgeshi da ita shine, hakkuri, ladabi girmamawa uwa,uba addini, gashi ba ruwan ta da duniya, Don dai ya fahinci cewa Maryam irin matan nan ne dake kona mutum farat daya, Don duk abinda zakai masu da wahala su tanka ma akai, Maryam ce zaune tare da Safiya agaban anty dije wace mamaki ya cika,ta, Ledan safiya ce akafara zazagewa inda sukaga wani dogon riga da turare guda biyu, sai kudi zube sabbi kar dasu, zasu kai kimani dubu dari koda hayi akai, Sai kuma aka jawo ledan Maryam, wanda ke dauke da wani dogon riga baki mai kyau da kuma rigar barci irin ta matan turawa, Wanda da kasa zai iya baiyanawa mace tsiraicin ta, Turare kusa kala biyar sai kuma wani dan kit mai dauke da dankune da sarka, Sai kuma kudi dollar's na America, sabbi ful da su suka zubu a cikin wani dan takarda, Duk kan su mamakine ya cika su don ganin wanan irin kyautar na bajinta da Sonny yai masu, Duk kan su sun rasa bakin magana saboda yawan kayan da tsadan su, Anty Dije ce ta numfasa tace a karo na farko tunda suka bude kayan kwasa ki samin a leda safiya har Yusuf ya shigo, Daga haka suka,watse kowa da abinda yake sakawa a zuciyar shi, Gurin mahaifin Yusuf din suka fara zuwa wanda yai mamaki kwarai daganin Sonny din a gatin su, Saboda sanin da yayi ko waye mahaifin Sonny din dakuma sani shi kan shi Sonny din, Sosai yaji dadi yai kuma alfahari da ganin su atare da dan nashi, Abin sha yasa aka kawo masu amma sam Yusuf ko ruwan su bai taba ba, Sai mai faman danne dannen wayan da yake yi abin shi, Shi dai Sonny din ne ya tatuli giyan shi sosai ba tare da wani buguwa ba, Bayan sun dan dauki lokaci a tare da tsohon ne inda yake bukatan Sonny da yadan ziyar ci church din su don special prayer, Ba wani mussu Sonny din yace zai yi kokari yazo kafin ya koma, Da haka sukayi mai sallama inda yake tajin dadin a cikin rayuwar shi, Zaune suke su biyu a falon shi Yusuf din sai TV dake ta kara shi kadai, Kowan su da abinda yake faman yi a cikin systems din shi, Sonny wanda ya kasa shakat da,samun sukuni a cikkin zuciyar shi tun ganin da yaiwa maryam ya dan yi gyaran murya, Wanda hakan yasa Yusuf dan dagowa daga abinda yakeyi , Ya dan wani marai,raice muryan shi yace pls, Joseph , Ina son ka taimaka min duk da nasan cewa abune mai wuya agare ka yanzu, Don nasan muna da bambancin addini, but idan har ka iya la,akari da cewa wanan ba komai bane Just life ne, Nasan cewa zaka iya taimaka min, for a few times, Yusuf wanda ya tattaro hankalinshi yana sauraron Sonny din don jin ko may yake da bukaya agurin shi har yake mai haka, Don shi azaton shi Sonny yafi karfin ya bukaci abu agurin shi bai samu ba Tambayan shi yayi cikin karaji da cewa just go a head tell me whay you want, Saida yadan lashe bakin shi sannan yakai kallon shiga kwaya Idon yusuf da idon shi da suka kada sukayi jawur, Yace I just want you to barrow me that your fiancée,,,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [4/28, 5:39 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Cikin wani irin zafin nama, Yusuf ya dago kan shi yakai wa Sonny kallo, Idon shi sunkada sunyi jawur kamar garwashin wuta, Sai kalman Innalillahi ya ke iya mamaitawa,a cikin zuciyar shi a lokacin, Ji ya,keyi tankar, yai tako guda ya,shake Sonny din har lahira, Kirjin Yusuf har wani irin bugawa yakeyi ya rasa ma awani duniya yake duk idon shi ya rufe a lokaci guda bai ganin komai, Kalman nan ta Innalillahi da ta zauna mai a baki, itace yake ta nanatawa a cikin zuciyar shi, Sonny wanda sam bai kula da irin halin da Yusuf din ya shiga ba alokaci guda, Yusuf yadago kai da niyar yiwa Sonny din wani irin mugun zagi, Amma sai Sonny din yace "Yes, cikin irin nuna ko in kula din nan, Yusuf yakara jin wani irin tukukin zafin rai ya taso mai tankar ya make bakon nashi mai halin Dan Akuya, A hankali Sonny ya,furta I really want to meet her again, I want to ask her some question a bout her religion,, Yaci gaba da ce tace gaisuwa da shi addinin ta ya hana don haka yake son jin karin bayani, Saboda yasha gani others Muslims girls suna sharking din hannu da su, Sai a wanan lokacin Yusuf da ke jin kan shi tankar wani namijin zaki yadan ji sassauci a zuciyar shi, Kan shi ya dukar kasa tankar badashi Sonny din ke magana ba a lokacin da irin yadda yake ji, Sai zuwa yan mintuna,masu yawa Yusuf yace cikin dasasshiyar murya, Aiko da baka gan ta ba ni zan iya yi maka bayanin abinda kake nufi,, Sonny wanda bai so jin hakan ba don shi maryam din ce yaso taimai wanan bayanin da bakin ta, Sai da ya dauki cup din ruwan sanyin dake gaban shi yadan kurba a hankali, Sai ya dan ja numfashin shi kadan yace wa Sonny kamar yadda kasa ni cewa duk wani addini bai yarda mata da maza su dinga cudan ya guri guda ba, Sonny din yadan ce Ok, Yusuf yaci gaba da bayani ya ce mai Allah ubangiji ya umurci, Annabin rahama, da ya hani mata akan cudanya acikin maza, Su zauna a dakunan su su yi ibadan su, Sannan su boye tsiraicin jikin su ga kowani irin namiji, Hat ta muharramin su ba ayarda yaga wasu sassan jikin su ba idan bada wani dalili ba, Sonny yana kada kai yace, Ok, Yusuf yaci gaba da maganar shi yana cewa don haka kaga ashe duk macen da kaga tana hurda a cikin mazaje, ta kaucewa addinin ta, ne, tana bin ra,ayin son zuciyar ta, Yakara da cewa duk diyan musulmuz jai mata ana haihuwan su tare da wanan sunnan a cikin zuciyar ta, Sonny wanda ke ta sauraren shi tunda yafara bayani, Yai wani irin numfasawa, saboda sharhin da Yusuf ke mai akan kamun kai na "ya mace,, Yace to duk mata daga mata har har tsofaffi da yan mata, Yusuf wanda yakara kai cup din ruwa a bakin shi ya kada mai kai yace eh, hakane, Wow inji Sonny din wanda ke wani lumshe idon shi don jin abin mamaki daga gurin abokin shi, Gani yakeyi Yusuf din ya jefa kanshi cikin addinin da babu freedom ko kadan, Don may za,a ce har yara kanana irin su maryam basu da freedom din rayuwar su, Baiko karasa,saurare ba wayan shi tai kara hakan yasa suka watse daga hiran da suke yi, Wanka yafito yana daure da dan karamin towel,, a jikin shi sai dan karami da yake goge ruwan da ya kwanta mai a suman kan shi yake dan tajewa a hankali, Kamar wanda aka sawa tunane a cikin rayuwar ta, A yadda yake ji yanzu, ko da zai rasa rayuwan shi akan taimakon a addinin shi zai yiwa musulunci hidima so sai, Dan haka ya karkare shirin shi yana mai aiyana abubuwa da dama, Wasu dinki ne irin zalekar nan wando da riga masu laushi, da santsi, Falon gidan ya fito inda yasamu har ankawo masu abinci daga gidan Anty shi, Shima Sonny din a cikin shigar kanan kaya yafito daga dakin da yake yana saye, da, wani dan farin glass a idon shi, Gaba daya saman dining table suka nufa don su ci abinci sun fara bada wani dadewa ba sai sukaji, Sallama a bayan su, koda Yusuf bai juya ba yagane cewa Aisha ce da kawar ta, Cikin wani dinkin buje da riga na shadda kowacen su take, Dinkin ya wani matse masu jiki duk ya fitar masu da suran jikin su, Nonon su duk ya wani turo kamar a fili a gaban rigar, da suke saye dashi, Sonny wanda don burgewa baiko iya kauda idon shi a kan su, Har zuwa lokacin da suka karaso gurin da su ke zaune, Aisha ta taso gadan gadan da niyar zuwa ta rungumi Yusuf, Cikjn wani murya mai kama da ta tsohon soja ya daka mata tsawa, Cak ta tsaya guri guda tana mai wani shu,umin kallon, Cikin muryan shagwaba tace mai haba Joe, may ye haka dan Allah, Yaushe rabon da in gan ka ne wai pls ? Da har zaka hanani hugging naka, Takara she maganar kamar wata yar karamar yarinya, Hey, girls' inji Sonny inda yake kokarin nuna masu seat, don su zauna, Wani irin mugun zama suka yi sun wani turo boom din su baya yai wani tare kaman kayan wanki, Nonuwan su ya wani turo gaban riga kamar yan matan clubs, Yusuf wanda sam bai kaunar ya kara daga kai ya kalle su saboda sun bala,in zube mai a fuska har zuciyar shi, Suna wanan betsere, betseren suna wani jan ra,ayin maza, A gaban su Sonny yake tambayar Yusuf cewa su wayan nan yan matan addinin su daban ne da na su maryam ko ? Yace cikin rashin fahinta yana nuna hakan da hannun shi, Duk da sundan fahinci may yake nufi hakan bai hana su ci gaba da shakiyancin duniyan da suka sa gaba ba,,, Nan suka kare, watsewan su inda Yusuf yagaji yai masu kora da hali sosai amma sai Sonny wanda yaji dadin kasan cewa dasu yai masu alheri irin ta bajin ta, din nan, Fita sukayi inda suka fara nunawa Sonny cikin gari, Jibrin kusan shine mai yiwa Sonny bayani akan irin al,adun kowani culture da yake tambayan su akai idan ya gani, A gajiye suka dawo gida don haka sallah kawai Yusuf yayi ya haye gadon shi daniyar ya kwanta ya huta amma sai yaji sam ba zai iya ba, Batare da yaji muryan maryam din ba, Hello little mummy, yawani shake muryan shi tankar dan yaro, Maryam wace a lokacin tana zaune gaban mirrow dake dakin nata tana dan shafa mai a jikin ta, Ta sauke wani lalausar murmushi wanda har Yusuf din yaji shi daga inda yake, Sai da hakan shima yasa shi yadan lumshe nashi idanuwan a hankali, Ya gajiya uncle maryam din ce take tambayar shi a hankali cikin nuna kulawa, Bari kawai maryam wanan bakon nawa duk yasa ni gajiya wallahi, Komai sai ya kwankwance shi kamar tsohon bature, ko likita, Tausayin shi maryam taji a irin yadda yai magana, A hankali tace mai kasan ance bakon ka Annabinka so kayi hakkuri dashi har lokacin da zai koma, Jikin shine yai sanyi a irin yadda maryam din tai bayani kuma gaskiyane zancen ta, Sai a lokacin yake tambayan ta Anty Dije, wace, ke ta faman tambayar shi tun safe, Tadan lumshe ido kamar yana ganin ta a fili tace, Tunjiya da muka dawo take ta tambayar ko yaushe zaka shigo , Yanzu haka tana falo a zaune nasan kuwa kila kai take dan jira agurin, Ya Sallam yace wallahi maryam har na kwanta saboda gajiya, Gashi kuma naji ido na kekas don rashin barci, saboda gajiya, Gabobin jikina sai ciwo suke min kamar nayi wani aiki mai yawa Cikin wani irin kararan murya tace Allah sarki, idon ta nan da nan yai kamar ya kawo kwalla, Tace cikin kariyar murya kamar ta mai kuka uncle kasha magani ko? Bawai magani zan shaba ai da ace zan samu wanda zai mun dan taushe a hankali , a hankali da kila bazan kara ko minti biyu ba zanyi barci, Kai uncle inji maryam cikin wani irin murya mai nuna tausayi maryam tace, Kasha magani za ka rage jin pain din da zaran ka sha, Maryam yakira sunan ta cikin wani irin murya yace, Nidai fatana Allah yasa baba ya idda nufin shi akan mu batare da ya canza shawara ba, Runtse idon ta tayi daga i nda take tana maijin kunyar abinda yafadi yanzu din, Kamar yasan abinda takeyi yace, Yes, ina son duniya ta sheda cewa ke din ce mata, ta halas, Sai kuma yadan ma rai,raice muryanshi ya ce maryam kiyi hakkuri ki rike Yusuf dinki amma, Ki gwadawa duniya cewa Furen Juji dane kamar kowa, Addini bai ce a kyamace shi ba kamar yadda wasu ke ikirarin hure maki kunne akaina, Hawaye ne masu dumi suka zubo a idon maryam din, Nan da na ta ringa she,shekan kuka kamar ya fada mata wani magana na daban, Dif ya kashe wayan shi saboda ba zai iya sauraron wanan kukan da maryam din shi ke yi ba a yanzu, Cak ya kashe wayan ya wurgata gefen filon dake saman gadon shi, sai kawai yashiga cikin damuwa, Tausayin rayuwar su yaji da shi da ita maryam din ,don yasan cewa tayi hakkuri sosai tayi biyayya ga mahaifinta, Rayuwa abin tausayi ce gare su shi da maryam sam bai taba tunanen cewa zai so wata mace irin yadda son maryam din yashige shi haka a lokaci guda, Tafe a motocin su sun fito wani kauye kallon wasu irin shanaye da Sonny din ke so, Yusuf sai sauri yakeyi don su karasa wani kauye mafi kusa don su samu sallah jumma,a, A wani massalacin kauye da yacika makil da jama,an musulmi suka parker motocin su, Don su samu gabatar da sallah su ta jumma,a a garin, Sonny kawai suka bari a motar inda yake kallo yadda kowa ke sauri don kada a wuce shi, Abinda ya kara bashi mamaki shine da mai, arziki da talalka duk guri guda suke tsayawa su hada kafadar su, Har zuwa lokacin da suka idar yana kallo yadda mutane kebawa juna hannu suna musabi,a, Sai bayan sun shiga motocin su har sun yi nisa ga tafiyan su ne Sonny ya jefowa Yusuf tambaya, cewa, Yaga duk guri guda suka tsaya sai mutun guda dake a gaban su, Tokin motar shi yake yi a hankali batare da yace mai uffan ba, Sai da suka danyi nisa kadan kamar ba zai yi magana ba sai yace wa Sonny din batare da ya kalle shi ba, Addinin mu addini ne mai bawa kowa yancin shi batare da nuna bambanci ba ga komai, Sonny din yace O, I See, Harzuwa lokacin da suka kai cikin gari a gajiye daboda nisan kauyen da suka tafi, Inda Sonny din yai ta hotuna da shanaye da fulanin rugan An kai shi gurin wasan dawakai inda Sunny din duk yarude saboda yadda yaga dawakai lafiyayyu sun koshi sai harbin iska suke yi, Washe gari ranan Sunday aka kaishi Church inda mahaifin Yusuf tare da, sauran members suka ji dadin zuwan shi gurin su, Yai masu kyauta ta bajinta inda sukai ta ihu suna cewa praise the Lord, Tare da,shi suka kwashi rawan su a wanan satin inda shi bawai abinda sukeyi ya damay shi bane, Sai Sonny yafidda rayuwan cewa zai kara ganin maryam kafin yabar garin , Don ya fahinci Yusuf bai ra,ayin haka a rayuwan shi sam, hakan yasa shi fita zancen kwata kwata, Duk da yaso ace sun wuce batare da ya kai bakon nashi gurin Anty nashi ba amma sai yaga rashin dacewan hakan, Hakan yasa shi biyawa dashigidan bayan sun dawo wani kauye wurin kallin yadda suke noman su a,local, way , A kofan gidan suka dan tsaya inda yusuf yai ta rafka sallama sai zuwa can yaji muryan matar gidan ta karba mai, Kusan a tare suka shigo su uku gidan shi da Sonny da Jibrin, Anty ce ta tare su cikin kwaliyan wasu shadda kamfala dake ajikin ta, Sam maryam bata,san da shigowar su ba tana saye cikin dinki atamfa buje da riga da,sukai mata dagwas a jiki, Yusuf naganin ta ahaka wani irin kishi ya ziyarci zuciyar shi ya rufe mai idon shi, Saidai bai bari sun fahinci halin da ya ke viki ba saiyadan basar da hira da antyn shi, Shiko Sonny yana ganin maryam sai ya shiga washe baki yana mai kokarin jan ta da hira, Sanin halinta ya dan sa Yusuf sake dan jikin shi don yasan irin hanlin miskilancin maryam din, Dan wake da mai da yaji sukayi don suci don haka,shima Sonny ya zauna ya kwashi wanan girkin har yana akaro mai, Sai kuma daga baya hira so sai sukayi indayake tambayar su akan musulunci su dan bashi bayani, Banda Yusuf wanda ke charting da maryan a lokacin, Yana fada mata irin yadda yaji lokacin da suka shigo gidan, Sonny ya koma bayan irin dibin alherin da yaiwa mutane taban mamaki, Bayan yakoma sauth korea ne Yusuf yai mai waya don yaji ko ya sauka lafiya, Anan suka dinga hira sai kusan karshe ne Sonny yake cewa Yusuf ai tun da yadawo zancen da sukaui na cewa ya canza addini zuwa ta islama gaskiya yashiga zuciyar shi, Yaji kuma zai koma din amma on one condition zai koma, Yusuf cikin jin dadi dafarin cikin jin cewa Sonny zai shigo Islama yace , Yace cikin karagi ya fada mai ko manene wan condition din, Sonny yace yana rokon shi alfarma da yabar mashi maryam ya aura, don ta taimaka mai gurin fadakar da addinin shi,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [4/28, 5:40 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Ina, rokon Allah Ya saukar da Albarka, Alkhairi,Falala, Wadata, Ni'ima, Gafara, Rahama, Lafiya mai amfani, Kwanciyar Hankali a garemu da Zuri'armu, da Musulmai Baki dayan mu Masoya FUREN JUJI,,, Yusuf wanda ya kai wani lokaci agurin da yake zaune ba tare da ya motsa ba Saboda mamakin maganar da Sonny din yai mai yan mintituna kadan da suka wuce, Hamdala yai ga Allah ubangiji subbahanahu, Wata,allah, Da ya kaddarace shi da ansa kalman shahada yafitar dashi daga cikin kafirci, Idan ba halin rashin imani a zuciya ba may zai sa Sonny ya tunkare shi da wanan zancen,, Na jahilci watau badan Allah zai musulunta ba ke nan don biyan bukatar shi ce kawai,, Wanan maganar yasa tunawa da wani Christian dan church din su wanda, Yai ridda har sau uku saboda jahilci inda ya zama Christian sai ciwo ya wuce daga jikin shi, Idan ya koma musulmin shi sai ciwon yadawo mai sosai fiye da farko,, Sai in har ya koma Christian zai samu sauki acewan shi wai a church ne saukin nashi yake, A haka har ya mutu cikin Christiatanci, batare da ya farga da cewa taimo yaje samu daga yan churches da kulawa fiye da zaman shi a cikin musulmi, Wani irin ajiyar zuciya Sadiya tayi bayan tagama jin labarin da fauziya ke fada mata, Akan irin alherin da Yusuf tare da abokin shi sukayiwa mutane a ziyaran da suka kawo, May Yusuf ke nufi da ita ne yanzu, sam babu ita ke nan acikin tarihin rayuwar shi, Wanan abin yai mata ciwo duk da tasan cewa kanin mahaifinta ne yai mata silar wanan sherin, Tabas yazama dole tamike tsaye ta san abin yi kafin wankin hula ya kai ta dare, Tamike tsaye tana gyara gyalen da ta sabalo a wuyar ta, Tana cewa kwanan nan zai dawo gare ta don ba laifin ta bane ai da zai dauki tsana ya sa mata Ita har gobe tana so shi don haka bazata iya hakkurewa da shi ba, a rayuwan ta, Ta,dan ce a hankali tabbas sai ka dawo da kafan ka, nice dai matar taka, don ka sani,, A hankali gudu yake shararawa saboda yana sauri kada rana tai mai bai isa da guri ba, Ganin ya fara hangen garin Kano' din yasa shi dan rage gudun da yake yi, Next kauyen da zai iya sada shi dagarin kano din yaga dan dan,dazon mutane a bakin titi ga wani mutun tallabe a jikin wasu matasa, su biyu, Duk motocin dake gaban shi sun wuce batare da sun tsaya ba, Tun daga nesa idon shi yahango mai abinda ke faruwa sai dai zuciyar shi tabashi ce inda muggan mutane ne baizaiga wanan taron ba acikin gari haka, Yusuf, wanda ke cikin motar shi yana tafiya a hankali, yazo gab dasu ya tsaya, Baka jin komai sai kiran da ke tashi a motar da kamshi da sanyin A,C, Kafin ya sauke glass sai,ga wani dattijo mai farin gashi jefi,jefi akai yadan leko shi, Yace dan Allah malam ka taimaka muna da wanan bawan Allah zuwa cikin gari asibiti za a kai shi, Ba musu ya bude masu security din motar sai motar ta bude, Har zasu shiga sai yaji muryan wani daga waje gurin mutanen yana cewa kai amma dai ku baku da hankali, Kuga mutum haka cikin wanan irin motar shine har zaku tare shi batare da,kun san kowaye ba, Kudibafa ku gani lafiyayen mutun yafito neman kai kamar makafi kun wani fadawa har kai uku, Murmushi Yusuf din yayi kawai sai,da yaga alamar cewa sauran mutanen sun dan tsurata da zancen mutumin, Saida ya lumshe idanun shi sanan yace masu , duk da ba,a gane macuci a fuska, Ni saboda Allah da Annabi zan taimaka maku amma fa idan kun yarda, Tsakanin su aka dan yi jimm sai wani daga cikin diyan mara lafiyan yace Allah ya tsare ku gyara mu shiga kawai, Tafiya yake yi dasu a hankali yadan yi yana waigen tsohon dake ta Nishi sama, sama, Tambayar su ya yi wani asibiti ne zaku kai shi, ? Nan suka fara muhawaran asibitin da ya fi saukin ganin likita, da kuma saukin kudi, Don haka, Yusuf yace may ke damun baba din ne. ? Yaron nashi wanda alama ya nuna cewa shine babba daga cikin su yace, Yau kwana biyu bai fitsari bai bahaya, Subbahanallahi inji Yusuf din cikin dan rudewa,, Yace akwai wani asibiti ne da kuke ganin ya na da kyau mu tafi can,? Ganin cewa mutanen kauyawa ne yasa shi dauko wayan shi, Noban Alhaji sambo ya kira yana bincikan shi ba bata lokaci yai mashi kwatance, Basu wani shawuya ba ga kwatancen da akai masu, Yusuf wanda yazo kano harkan business din shi sai gashi ya buge ga zirga,zirgan asibiti, Dashi akai komai, har zuwa lokavin da likita ya zo yadiba tsohon dake ta kugin wahala saboda azaban da yake sha, Dubu sittin da yan kai likita yace su fara bayarwa tukun , Zasu tsaya inda,inda Yusuf ya jawo yan dubu, dubu daga aljihun rigar shi ya mikawa likitan, Ba a fi wasu yan mintoci ba aka jaye mai komai yasamu sa, ida, Gado a,kabashi don haka Yusuf din ne yakara biyan sauran kudaden da ake bukata, Tun safe sai zuwa bayan sallah azahar ya samu kan shi, Sai, a lokavin yashigo dakin dakin bayan ya gaishe su a mutunce sanna ya gusa gurin tsohon da yaji suna kira da malam yai mai sannu ya jikin, ? Malam din yadan dago kai, zuwa gurin da Yusuf yake tsaye daga gefen shi, Hannun shi yadago a hannkali ganin may yake nufi ne yasa Yusuf din saurin mika mai nashi hannun, Yarike hannun jimmmm har zuwa wani dan lokaci bakin shi kawai zaka ga yana motsi, Sunan shi ya tambaya yace mai Yusuf yake, sai tsohon ya dan gyada kai alamar gamsuwa,, Kokarin wucewa yayi bayan yai masu sallama, daya daga cikin su ne yai a,zancin karban nomba Yusuf din da sunan zasu kirashi suyi mai godiya daga haka yai masu sallama, ya nufi gurin da zai sauka,,,,, Kwance take saman gadon ta tana barci amma sai juye juye takiyi daga kwancen, da take din, Gudu take tayi a,wani bakin daji mai duhu da kuma, sarkekiya, Rigar barcin dake saye a jikinta shine saye gareta a cikin mafarki, Gudu kawai takeyi sai wasu halittan da bata taba ganin irin su ba ke bin ta a guje, Hakin da takeyi agudun shine ya baiyyana afili tana ta juye juye, Tana gudun tana cire wanan yagwagen dake sarke mata hanya da jikin ta, Bakin wani rami suka kawo ta inda taja ta tsaya guri guda, Gani cewa wa, yanan halittun sunyo kanta gadan gadan yasa maryam din kara hannayen ta biyu ta rufe jikin ta zuwa fuskan ta, Tare da furta Innalillahi cikin wani irin murya mai karfi, Wanda har mueyan yakai dakin da Anty dije take tare da dan ta Abubakar da maigidan ta, da yazo kwana biyu da suka shige, Wanan sautin da Anty Dije da maigidan tasuka ji na maryam shi yasa su taso cikin sauri zuwa dakin da maryam din take kwance, Jikin ta ya jike kamar wace akaiwa yayafin ruwa akai, Jin karan bude kofan su anty yai daidai da saukowan ta saman gado da karfi , Inda tayo kan Anty nata cikin kaduwa tana kokarin shigewa jikin ta a tsorace, Hakalin Anty Dije ya tashi matuka saboda irin halin da, ta ga kaunar nata a ciki, Don haka sai ta rugumay maryam din a jikin ta inda take ta maida numfashi guda guda a tsorace, Dakin suka fito da ita zuwa falo inda sukabar mijin na Anty yana yan dube dube a dakin kamar wanda ke bidan wani abu, a dakin, Kusan a nan suka karasa kwana falon inda har da yaran suka kwaso zuwa falon, Dakyat suka ga safiya da maryam din saboda irin halin firgicin da ta shiga ciki a lokacin, Tun a massalaci gurin sallah Asubah mijin Anty ya shedawa baba abinda yafaru da maryam din a daren jiya, Gida baba ya koma ya gyara shiryawa ta re da zuwa gurin, wani aminin shi malami ne, Malam na, Ngaski, inda yai yan abubuwan su na malamai, Daga karshe ya danyi rubutu yasa a cikin wani leda yace abata tasha zata samu barci, Hakan akayi kuwa don dai maryam din ta samu barci sosai har da kuma zafin da jikin ta yayi duk ya rage, Sai zuwa kusan la,asar tasamu tadan mike, ruwa ta watso a jikin don takara jin karfin jikin ta, Bayan ta dawo tasamu anty ta hada mata abincin ta , Saida tai sallah sanan ta samu guri ta zauna tafara dan tsankwaran abincin a hankali, Mafarkin da tayi ne yafado mata a rai irin yadda tai ta gudu acikin wanan bakin daji, Siffofin wa yan nan miyagun namun dajin da tagani su yo kanta yasa ta saurin zabura da karfi tankar a lokacin ne abin ke faruwa, Anty ce cikin fadar Wa,iyazu Billah, maryam ki dinga karanto addu,a a bakin ki pls, Hakan yai daidai da shigowan baba gidan wanda yake dauke da wani bakin leda a hannun shi, Anan ne yadan murmusa yace Allahu Akbar watau duniya abin tsoro ne Dije, May Maryam ta tarewa mutun da har zai sata gaba haka yarinyar da naga bama fita takeyi ba, Karbi wanan maza bata tashanye kuli guda gaba daya yanzu ta, shafa sauran ajikin ta, Dayan kuma da dare idan zaku kwanta sai ki bata Allah ya kyauta, Duk sukace amin alokaci guda tare da karban kullin suna budewa Mahaifin nasu ya dan kalli yar tashi wace take hankali a tashe duk ta wani ramaywa a lokaci guda, Yadan gyada kan shi alamar takai ci acikin zuviyar shi fam, Addu,oin tsari ne ya kara nanata mata idan zata kwanta tare da cewa insha Allah zata daina ganin abinda take gani, kuma Allah zai kare ta daga duk wani maisheri, Daga haka ya mike zuwa yai madu sai da safe, Yusuf wanda yake masaukin shi zaune ga abincin da aka kawo mai ya sa agaban shi amma yakasa cin komai, Tunane duk ya addabi zuciyar shi kamar yai ihu ko zai samu relief a lokacin, Sakon da Sonny ya kara turo maine akan zancen yana son musulunta am.a sai idan Yusuf zai bar mai maryam a matsayin gift din shi na shiga musulunci, Wani irin nisawa yayi tare da runtse idon shi da suka kada mai sukayi jajir alokacin, Kara bude su yayi inda ya kurawa labulen dakin ido kamar mai son gano wani abu a cikin dakin, A gaskiya yana son musuluntar Sonny do min wani babban jahadi ne a gare shi, To kuma ya zaiyi da dakon son maryam da yakeji tun tana yar ficiciyar ta,, Wanda sai a yanzu ne ya gane cewa So ne yake mata shi yasa yake kin duk wani al,amari na,ta a wancan lokacin,, Idon shi yadago ya bude inda yaci gaba da nazarin shi akan abinda ke damun shi, Ya san halin Sonny sosai yana daga cikkin ire iren mutane yan son rayuwa wa yanda sam sukan manta da akwai mutuwa, Gashi kuma matashi ajin farko masu fada aji a kowani, kasa, Duk inda suka kyalla ido suka ga mace har sukaji suna son ta tofa sai sun lasa suke iya kyale ta, Wani irin kishi ne mai karfi ya tukako zuciyar Yusuf saboda tuna kowa ye Sonny din da yayi, Maryam din ce ta bashi tausayi a yadda yake ganin cewa duk laifin shine da ya kawo shi inda take, Inda zuciyae shi tai dan sayi shine tunawa da yayi da kowace ce maryam din, Shi kadai ya murmusa don sanin kowace maryam din dayayi da sanin halaiyanta, Maryam yarinya ce da tasan ciwon kanta, wace abin duniya bai taba tsone mata ido, Ga tada kau da kai ga abin mutum don shi duk iya sanin da yai mata bata taba cewa tana son wani abu agurin shi ba, Ire iren wanan tunanen yai tayi kala kala inda daga karshe ya yanke shawaran, abinda ya dace yayi akai, Jiki ba kwari haka ya mike daga gurin da yake zaune saboda shawaran da ya ke ganin itace kawai mashi mafita, Ya hana shi sukuni a zuciyar shi don haka wanka ya fada ko da zai ji sanyi a zuciyar shi, Ga abinci a gaban shi amma sam yakasa koda spoon guda, ne saboda irin yadda yake ji, a zuciyar shi, Dan tsohon da ya taimakane ya fado mai a rai saboda yana da bukatan yayi ko ya jikin nashi Kira na biyu aka daga wayan da sallama bayan ya karba ne, Yagabatar da kan shi a gare su nan da nan suka sheda shi,. Godiya suke mai shikuma yana kokarin tambayar su lafiyan tsohon su, Nan dai yai masu alkawarin cewa zai dawo ya ziyarce su zuwa gobe idan ya rarage abinda yakeyi, Maryam tana zaune duk tunanen rashin jin muryan Yusuf kwana biyu da batayi yana daga cikin abinda ke dan damun ta, Bata san may yasa ba yanzu take yawan jin shi a jikin ta fiye da tsan manin ta, Muryan Anty Dije ce taji a kan ya tana tambayar ta Maryam lafiya dai ko ? Bakomai tace wa yar nata, Bakomai nagan ki haka a zaune cikin damuwa maryam,? Yar mursmuhin mai kama da yake ta sake kawai, Kodai Yusuf kike tunane tunda naga jikin ki dai kin ji sauki yau, Mamaki ya cika maryam din don jin abinda yar nata tafadi, Kai tagirgiza tace haba dai Anty may zan yi tunane gare shi, Anty dije wace bawai ta yarda bane tace bam san may yasa wayoyin shi suke a rufe ba, Duk layin shi nakira akashe suke tun jiya da safe, Don haka nima ina tunanen ko lafiya yake amma barin kira Jibrin muji, Jibrin din ne ke sheda ma su cewa yatafi kano gurin wani meeting ne amna zuwa gobe zai dawo Insha Allah,, Sai alokacin maryam tai dan ajiyan zuciya har yar nata taji, Amma sai bata ce mata komai ba wucewa kawai tayi zuwa cikin gida abin ta, Gurin da take zaune tadan kai kwance anan barci ya dan kwashe ta, batare da tasani ba, Anty Dije wace ke kitchen tana tuka tuwo muryan maryam dake barci a falon ya katse ta daga tukin tuwon da takeyi, Wani irin kakakari da shure, shure takeyi kamar wace ake zarewa rayuwar ta, Sosai Anty Dije ta razana saboda ganin yanayin maryam din, a lokacim,,, ZEEE MAKAWA YELW@ [4/28, 5:40 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Ina rokon Allah ya nuna mu na, wanan Watan mai Albarka da Darajja, Ni,ima Gafara da Rahama, Ya Allah ka sa damu da Albarkokinan na shi, lafiya RAMADAN KAREEM👏👏👏👏👏 AMEEN YA ALLAH👏👏👏👏👏👏👏👏👏 A gajiye yake taka matakal ginan ya na saye da rigar shadda mai ruwan makuba Dinki rigar iya cinyar shi kawai da yar gutunwar hannu daidai gwiwar hannu, Saboda zaman da yasha gurin meeting din starching rigan yadan takure , takure, Kan shi babu hula sai sheki da yakeyi yaji oil ga kamshi, Hannun shi guda yana a cikin aljihun shi da sauri sauri yanzu yake tafiya don ya isa gurin motar shi, Tundaga nesa ya bude motar yana isowa yashiga, Fuskan shi ya shafo da hannushi yakara mayar wa har zuwa wuyar shi wani iska yafurza tare da fadin Ya Allah, Yana daukar waya kiran anty dije yana shigowa mashi, Sai a lokacin ya dan yi ajiyar zuciya a irin yadda yake ji, a zuciyar shi, Sallamu Alaikum Anty Sorry zan kira ki dan anjima kadan pls, ina saman hanya ne, Bata aje wayan sai fada data haushi dashi cewa zai kashe waya haka har kwana biyu, Murmush mai sauti ne yadan sake saboda yasan cewa shi mai laifi ne sosai, Don haka yace gwiwa na a kasa Anty aimin afuwan pls, Kwanar asibitin da yanufa don diba tsoho ya karya batare da wani dogon tafiya ba ya isa asibitin, Tsohon yana kwance saida hannun shi guda yana daure da ruwa ana mai kari, Dan tsohon najin muryan Yusuf ya yunkura da niyar tashi, Gaba daya har Yusuf din suna hada baki gurin cewa ,a, a, a baba ka kwanta da ruwa a hannun ka, Tsohon yakoma ya kwanta yana cewa to, to, yana mai gyara kwanciyar shi, Yusuf ya matso gab da tson inda suka sa mai kujera ya zauna suna fuskantar juna da tsohon, Alokacin Yusuf yaji a zuciyar shi dama ace wanan tsohon shine mahaifin shi Dayafi kowa morewa, mahaifi a rayuwa da ba zai iya gusawa nan da can ba a wanan halin da zai tsaya ya kula da,duk wani motsi na shi, Yana zaunawa wanan tsohon yafara zuka mai albarka ya na mai fatan gamawa da duniya lafiya, Wani abu ne yazo mai a makoshin shi ya tokare mai yakama jin wani irin tukuki a zuciyar shi, Da kyat ya samu,ya hade wasu miyau masu daci, da yauki Sai yar dariyar yake yake yi a fuskan shi tankar ya kai mai ciki, Kai mutumin wani gari ne ? Tambayar da tsohon yajefo shi da ita ke nan a lokacin da yake cikin tunanen shi, Forgigit ya tuna cewa ko shi waye, Inda har za,a tambaye shi ba zai gushe da fada masu gaskiyan ba kamar yadda ya saba fada cewa Asalin shi FUREN KAN JUJI NE, Dayan yaron tsohon ne ke cewa ana tambayar ka ko kai mutumin wani gari ne wai,? Kwantagora ya ba da, ansa, a ta kaice ,,,, Wai, wai, akwai nisa gaskiya a cikin wani jaha garin yake dayan mutumin ke tambaya,, A can cikin jahar Niger garin yake, yankin yamma, Allahu akbar inji tsohon ya fadi lokacin da yake dan gyara kwanciyar shi, Saida muma zamane yakai mu can asali mu yan jahar,Benue ne, Gaba dayan su suka juyo da kallon su inda yake cikin mamaki, Yace musulunta nayi bada dadewan nan ba saboda fahintar musulunci itace hanyar gaskiya,, Gaba dayan su a lokaci guda sukace Allahu Akbar, Kan shi ya sunkuya kasa don abinda yake ji, a jikin shi tun jiya, Babu abin dake a zuciyar shi duk yinin yau kamar yadda zai furta hukunci da ya yanke a kan su, Dan tsohon nan na kwace cikin cijewa irin ta mai jin jiki, Tsohon yai ta bashi labarin ko shi waye da kuma yadda ciwon ya samay shi , Nan ne Yusuf gane cewa dan tsohon irin malaman nan na zaure ne masu tara almajirai da yawa agidan su, Zaune take cikin wani yellow material dinkin buje da riga masu kyau, Dan kwanlishi ba daurawa tayi ba just ta aza shi saman kan tane, Wayan ta yana a hannun ta tana dan yin game da shi,, Kirane ya shigo mata sai dai bata gane ko waye mai nombar ba, Da sallama ta dauki wayan muryan mace ce ke magana a layin, Maryam taji an anbaci sunan ta, batare da ta ansa ba taci gaba da sauraren mai maganan, Sai kuma mai maganar bata kara cewa komai ba dan shiru ne ya biyo baya, Tace baki sanni ba amma dai da zaki gan ni zaki sanni, Kiran da nai maki shine akan nasaban ki da Yusuf watau Joseph dan gidan Ema mai manja, Gaban maryam ne a lokacin yabada wani dam haka kawai batare da tasan ko may ye za,a fada mata, ba a lokacin, Wani,tsoro ne ya lullube ta da sauri tadan kama waigawa ko zataga Anty ta da ido, a kitchen ta hango ta, tana kada miya, Karo na biyu mai maganar ta kara ambatar sunan maryam din wanan katon kamar mai rada tai maganan Daidai lokacin da maryam din ta iso gurin da yar na ta take , Kada kiji tsoro maryam ki saurare ni da kyau kiji may zance maki, da kyau, Gaskiya ni bazan iya cutar da mutum dan uwana ba shi yasa naga ya dace in fito fili in fada maki abin da ke gudana akan ki, Wayan suka zuba wa ido daga ita har yar ta suna sauraron mai magana, A kofar shiga gidan ku an rufe wani abu wanda daga ke har Yusuf din indan kun taka kun rabu kenan har abada, Sannan kuma ba zai kara kula koda Anty kiba bale wani naki, Ke kuma ance a sakar maki ciwo mai kama da ta hauka ko batar hankali, Don kowa yazaci baki da lafiya ne shi yasa zai guje ki, Tagumi sukayi suna sauraro sai innalillahi suke ambatawa kawai, Inda taci gaba da masu kwatancen gurin da aka binzine masu abubuwa akofar gida, Anty ce ta tambaya cikin saurin jin datayi kamar mai shi tana kokarin rufe wayan ta, da cewa, A sake cikin sauti mai karfi tace yanzu may abin yi yar uwa, Mai maganar tace don girman Allah ku rufamin asiri kada ku bari agane cewa nice na fada maki wanan zancen, Tambayar ta Anty Dije takara yi akan cewa may ye mafitan zancen, Sai cewa tayi aje daidai gurin da aka bizzine abin a tone tun gudan su bai bi gurin ba, Don tun daren kwana hudu daya wuce, aka rufe abin agurin, Kuma wanda akaba kudi don yadiba koda maryam din tabi gurin yace har yau baiga fitan ta daga gidan ba, Kinga ke nan abin bai fara aiki ba ke nan ko tace cikin nuna kulawa, A sanyaye Anty Dije takewa mai wayan godiya sosai inda take cewa ai babu komai don duk ciwon musulumi na musulmi ne, Inda tace insha Allah idan taji wani abu zata kira su ta sheda masu da wuri, wuri,, don su dauki mataki, Maryam wace tun fara zancen idonta yaciciko da kwalla, Take,hawaye yafara mata sintiri a idanun ta take dan she,shekan kuka,, Anty don Allah ku taimaka ku jaye zancen nan tun ba,a halakani ba, Zan hakkura da Yusuf din don dama nasan cewa ba sa,an yina bane Kawai dai biyayyane nayi har na takai na fara jin shi a jikina, A haka ta dinga share hawaye da bayan hannun ta, Fuska a daure don jin abinda maryam din tace Anty Dije take kallon ta, tace wa yar uwan nata, Yanzu maryam ina imanin ki da tauhidin ki ya shiga da har zakiyi believed da wanan maganan, Kiyi imani da cewa duk abinda ya samay ki daga Allah ne maryam , Tunda har Allah yasa munji abinda ake yi akan ku kin ga sai kawai mu roki Allah ya kare muna ke, Da sauri maryam tadan kalli yar,uwar nata tana kada mata kai tace, cikin muryan kuka, Anty kawai dai a fasa wanan abin ni bazan iya ba gaskiya tun yanzu ace har an fara yiwayiwa mutun irin wanan sherin,, Tana kokarin share hawayen ta, sheshekan kukanta na tashi cikin tashin hankali, Murmushi Anty Dije ta yi ta girgiza kai, kaiyya maryam ai idan kince haka sun samu galaba akanki ke nan, A sanyaye maryam tace cikin muryan kuka, Anty to ya za,ayi, Anty Dije tace barin kira baba in sheda mashi abinda ke faruwa kafin abu yai nisa, Daga haka suka bar wajen cikin tashin hankali saboda duk sun shiga rudani, Yusuf ya kasa wuce saida aka sallami wanan tsoho ya dauke su zuwa, gida, Badon komai ba sai don ya fidda kan shi a zargin da suka yi mai tun farkon dauko su zuwa asibitin, Sosai mutanen kauyen sukayi mamakin ganin su tare da mutumin da sukayi zargin cewa dan yankan kaine da farko, Saboda mugun haduwan da sukaga yayi gashi matashi ga kyau ga kudi kuma, Nan malam yaroki Yusuf akan don Allah idan an kwana biyu yadawo garin yana da bukatan ganawa da,shi, Amma kafin ya wuce yasa yaron shi karami yai mai a wani rubutu a ruwa yace yasha, Yusuf wanda bai, so hakan ba azuciyar shi amma sai ya daure ya sha saboda biyayya kawai, Da zai tafi yakawo alheri masu yawa yai ma malam da jama,an shi sukayi sallama dashi cikin dadin rai, Sunkarbi nomban shi don su kirashi a cewar shi idan ya isa, A hanya ne ya ke tunanen kitan Anty Dije wace yaiwa alkawarin kira tun daren jiya, Ya so ne da kawai idan ya koma sai ya samu lokaci ya je kwantagora ya fadawa Anty irin shawaran da ya yanke a kan maganar shi da maryam acikin ruwan sanyi, Duk da yasan cewa akwai rikici a gurin baba don dawuya yadauki yar shi haka kawai yabawa wanda bai san asalin shi ba, Amma dai shi da kan shi zai fadakar dasu don su fahinta akan Sonny din, Duk da yasan cewa ko shi don sun san asalin shi dakuma irin cin fuskan da akai mai akan neman mace, In badon haka ba yasan cewa baza,a bashi ita ba sam saboda su talkawane da suka san mutuncin kan, su, Zaune take a gurin da tagama sallah isha,i amma tunane duk ya addabe ta azuciyan ta, Ba komai take tunane ba illa ta yadda za,a bullowa wanan bakon al,amari da yazo mata, Don dai ita a iya sanin ta batada abokin fada ko kuma hamayya, ako ina, Amma wai sai gashi kwatsan an wayi gari ana son a cutawa rayuwan ta, Wayan hannun tane ta daga don ta diba time, tagani, saboda tasan cewa da zaran angama sallah isha,i baba zaizo, Takwas da rabi taga don haka tamike tafara dan tattara kayan da tai sallah don kada baba yashigo bata a falin su,, Falon yai shiru, baka jin komai sai muryan Anty Dije kawai da ke koro wa baba da bayani tiryan tiryan, Kamar babu kowa a falon bayan ita, kowa da irin nazarin da yakeyi, daga baba har aminin nashi da sukazo tare, Maryam ce a gefe guda tsugune sai hawayen da take zubarwa akai akai, Baba kan lumshe idon shi yayi saboda mamakin yan Adam daya kama shi, Yasan cewa Allah ne ya kare mashi yar nashi saboda addu,oin da yake yawaita yi musu, akai akai, Yarinyar tana bashi tausayi saboda yasan cewa akan shi ce tai biyayya Wani irin mugun tausayi tabashi da yadan kalle ta da,wutsiyan ido yaga irin yadda take share hawayen dake sintiri a idon ta, Abokin baba ko ince aminin shi kuma makwabcin su, yai murmushi cikin gyada kai bayan ya gama jin bayanin da Anty tai masu kaf, Yadan kalli inda baba yake yace, ina kon kwanto, amma ai babu komai idan har sun san wata aibasu san wata ba, Don kaga Allah ne ya tona masu asiri don ya wargaza masu plan din su, Amma zasu sha mamaki don ta Allah batasu ba sherin su zai koma masu, Sallama sukayi wa su maryam din suka tafi tare da kwantar masu da hankali na cewa babu abinda zai faru da yardan Allah, Hakan yasa hankalin maryam ya da yar uwanta ya dan kwanta amma ba wai gaba daya ba, Koshi saboda sanin da sukayi wa shi malam na ngaski din ne cewa bakanwar lasa bane shima,,,,,, Masallacin Jumma,an ya cika saboda anan sarki ke sallah da sauran dattijan gari, Mahaifin jibrin da yawa daga cikin makwabtan su suna acikin sahun da suke kusan gaba, gaba, Bayan an idar da sallah jama,a suna kokarin wuce wane sukaji wani bawan Allah mai zakin harshe yana cewa don Allah a,dakata , Akwai daurin aure ga wanda Allah yaba ikon tsayawa, Hakan yasa jama,a da dama suka dan dakata don su sheda wanan daurin auren, da akai shela, Mahaifin Jibrin tare da, malam Abdulsamad suka matso kusa da liman nan shima Mahaifin su maryam tare da sauran yan uwan shi har su, mijin mahaifiyar ta da ya aikawa yana son yazo ciin gari a yau, Yakuma zo din duk suna gurin su malam A, A da su KB wanda shima yazo garin saboda matar shi da take dauke da tsohon cikki, Anan ka gudanar da shardan aure kamar yadda aka sharida wa musulumi, ci, da sha da sutura,, Sanarwa kawai sukaji mai fada na fadin cewa an daura auren Yusuf da maryam akan sadaki naira dubu hamsi, kacal, Inda mahaifin Jibrin din ya gabatar da kudin a hannun waliyin auren maryam din watau mijin mahaifiyar ta da malam aminin shi, Ba,a dauki wani lokaci ba wasu mutane suka gane ko auren wa akadaura a lokacin, Ciki har da A,A dasu KB da sauran abokan hurdan Yusuf din, Ba,karamin mamaki mutanen da suka halarci daurin auren sukayi ba don basu da wani masaniya akan zancen auren, shi,,,,,, ZEEE MAKAWA YALWA, [4/28, 5:40 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, YAURI YA,Allah, Ya Rahaman Ya Rahimee, Ya Maliki, Ya Salam, Ya Fattahu, Ya Haiyyu, Ya Kaiyyumu, Ya Malikil, Mulku,Zullani Wal,ikiram, Allah kasa mudace ya,Allah kasa mugama da duniyan mu lafiya, Allah ka rahama muna,👏👏👏👏👏 Kiran layin wayan shi yake yi a gagauce tun bayan minti goma sha da suka wuce, Amma layin baya shiga sam switch, off suke cewa tun dazu, Ba halin shi bane hakan sam rufe waya don haka yake mamakin abinda ke faruwa, Layin Jibrin ne yakira don ya ji ko Yusuf din lagiya yake ya kashe duk layin wayan shi, Kira guda layin Jibrin din yashiga sallama tare da yar raha kamar yadda,suka,saba, Amma wqnan karon Jibrin din kawai keyi shi KB yaki mayar, mai da martani kamar yadda,suka saba, Sosai abin yabashi mamaki don ba irin haka suka,saba yi a tsakanin su ba, Kai ina mutumin yashigane wai duk wayoyin shi a kashe tun dazu,? Au Yusuf kakw magana gaskiya ban da masaniya don dai jiya yana hanyar shi ta,dawowa kano mukayi magana, dashi, Amma yanzun nake son daga nan mosque in wuce gidan shi in mai sannu da zuwa, Ke nan kana da labarin auren shi kai ko ? Ban fahince ka ba in Jibrin wanda tambayar ta KB tazo mai wani iri, Aure ? Wayai aure kake nufi wai ? Ansa yabashi dace wa wai kaima kana nufin kace min baka da labari, Bayan mahaifinka ne yai waliyin auren da aka daura mai a massalacin jumma,a dazun nan, Mamaki kwarai Jibrin din yayi sai kuma ya kama tambaban ko da wace ce aka daura auren, Zaune yake a gidan inuwan wani ice dake cikin gidan man nashi can gefe guda , yana kallon duk wani mai shige da fice a haraban gidan man, Mutun biyune saman wata tsohuwan mashin suzuki blue, Tunda Mr Emanuel ya hango su ya daure fuskan shi, Saboda suna daga cikin masu zuwa gurin shi yawon maula, Hakan yasa yana hangosu ya daure fuskan shi saboda yana bakin cikin irin wanan halaiyan na irin mutanen nan masu yawon maula, Gaisuwa,sukafara dashi tare da tambayar lafiyan jikin sh, Daya daga cikin mutanen ne kecewa Mr Emanuel din wanda ya,daure fuskan shi tamau, don kada su ji dadin rokin shi, Mutumin yace ashe yaro ya yi aure shine muka ce bari muzo muyi ma murna, Mr Ema yace cikin kada kan shi wa ? Ummmmm, Ummm ba yalo namu bane, Shiru mutanen sukayi sai zuwa can gudan yace yaron kane mana wanda ya musulunta kwanakin baya, A,a yana kada kai alaman bashi bane, cikin daurewa fuska, Mutumin ya dage da cewa shine fa wanda akecewa Yusuf Joseph, Gaban tsohon ne yaba ba da damm, saboda bai taba zaton haka daga dan nashi ba, Indan ko har hakane plan din su akan Yusuf din ya rushe ke nan, Don tun da har yaji cewa anyi aure tsakanin shi da diyan musulmai, yasan cewa mawuyacin abu ne, kuma ya dawo cikin su , Don haka bai tsaya sauraren wani abinda zasu ce ba yadogara sandar shi ya mike tsaye, Fuuuu yabar gurin batare da ya tsaya takan mutanen ba, Inda haushi yakama su don su azaton su zasu samu kyauta a gurin shi, Kusan kowa da yadace ace ya kirashi a lokacin da ake bukata samun shi a layin amma layi. Nashi yana a kashe duk wanda yakira shi bai samun shi, A hankali yake saukowa a matakalan jirgin inda yake saye cikin bakar corth da wandon su, Bai riko komai ba a hannun shi sai wata yar karamar briefcase da ke rike a hannun shi, Enoc ne ya iso don taron maigidan nashi wanda yadan dade bai shigo Lagos din ba, Cikin farin ciki suka gaisa inda yake mai sannu da zuwa a cikin mutunci, Sun isa gida lafiya inda yasamu gidan shi lafiya lau kamar yana aciki ko yaushe, Wanka ya fada ya tare da dauro alwala, bayan yafito ne yai sallah tare da mikewa zuwa falo don yaci abinci, Cibi uku kawai yayi sai yaji karan wayan Enoc wanda matar shi takira a lokacin, Sai a lokacin wayar shi da take a kulle tun jiya tafado mai arai, Briefcase din shi ce yasa a miko mai yaciro wayan a ciki, Sakon nai da miscalls ke ta baiyyana a cikkn wayan nashi a lokacin da ya kunna ta, Sakon da yafi daukan mai hankali a,lokacin shine wanda akace idan yabude waya yakirashi pls KB da Jibrin, Cikin sauri yafara dialing din nomban Jbrin din amma busy yake, Don haka yakira na KB kb wanda yana gida tare da matar shi ya dauki wayan cikin fada yace, duk da sallaman da Yusuf ke mai cikin taushin harshe, Kaga daman kun,na wayan, yanzu ko ko angwanci baka fara ba amma ka fara kashe waya, Murmurs shi yaiwa KB din kawai batare da yasan ko may yake nufi da zancen shi ba, Yusuf yace kai anfada maka cewa kowa irin kane daga yin aure kakoma baka son zama gurin aiki, Na bincika ko kana Abuja ance min katafi kwantagora ai, KB ya din ce au dama sai jiya kaso ka fada min cewa zakai aure ko,? Aure inji Yusuf din wanda ya tambaya cikin mamaki, Kai kaidai kila sai na fada wa Jibrin cewa aima rukiya akan wanan auren da sha ma kai, Yusuf din ke fadawa KB din hakana, Jin called din Jibrin da yayi ya shigo yasa shi katse layin KB din don sam bai fahinci abokin nashi ba yau, YJibrin yace ango kasha mai,,,,, Hmmm yace kawai da ya ji abinda jibrin din ya fada,mai, Zancen ku gudane da KB din yau ashe yanzu ya bugo min waya ba wani abin da yake iya cewa sai zancen aure, Jibrin yakira Yusuf cikin wani irin soft voice saida Yusuf din yagane cewa something serious zaice mai, Ya akayi ne man inji Yusuf din ya tambaya cikin taushi, Kana inane yanzu inji Jibrin yana tambayar Yusuf din? Ina Lagos yace a,takaice kawai, batare da ya wani zaci komai ba, Shitt inji jibrin din abin yaba Yusuf mamaki don yasan cewa ba halin jibrin bane hakan,? Man wai wacece ka aura ne pls,? Jibrin din ya,sakowa Yusuf tambayan da yaji ta a bazata, Ban fahince kaba fa inji Yusuf din yacewa Jibrin din, Jibrin yace to be serious yau andaura ma aure a massalacin Jumma,a , What's cikin wani irin murya da har sai da ta razana Jibrin din, Gaakiya inji Jibrin yace a bisa wakilcin mahaifina da malam Abdulsamad WARA,FA,A,NAHU, MANKANAN ALLIYAN,, Yusuf yace a lokaci guda, Yai shiru can yace HASBUNALLAHU WA,NI,IMAL, WA,AKIL Jibrin yace wai kana nufin baka da labari Yusuf ko may wai ? A hankali cikin wata irin murya karara yace wlh banda labarin wanan zancen, Don ban masan anyi ba ni, Kit, ya kashe wayan ga sanyin AC a falon amma wani irin zufa ne yaji ya karyo mai a goshin shi, A hankali yadan rike gefen kujerar da yake a zaune inda ya fara hawan steps din da zai sada shi da dakin shi a hankali, Tafiya yakeyi kamar mai ko yon tatata, don da kyat ya ke iya daga kafan shi zuwa saman, Saman gadon shi yafada jagwal kamar wanda kwai ya fashewa acikki, Aure, Aure ? To da wacece haka da har ban sani ba , Idon shi ya mayar ya rufe a hankali, Aisha, no no Sadiya never yace cikin juya kan shi, Maryam maryam yakar furta wa a fili, sai yace sam ba,zata yarda ai muna aure a haka ba, Don har yanzu bawai ta yarda da shi bane ai balle a daura masu aure, Ina ba ita bace saboda sam hakan baima yu,yuwa ai don shi yanzu maryam tafi karfin shi zai barwa aminin shi kuma ogan shi, Wanda yakewa kwadayin shiga musulunci very soon, Who the he'll is she. ?,,, Maryam ta zaune gurin da ta idar da sallah tayi addu,an fatan alheri dakuma neman kariya agurin Allah, Tana jin muryan Anty Dije da yaran ta afolo suna magana akan wai abinci yayi yaji yau, Ita dai batace komai ba saboda damuwan dake damun ta a cikin zuciyar ta, Sallaman matan gidan su suka ji sai kuma abayan su baba matan guda tana dauke da kwandon goro a kan ta, Ànty Dije ce eace ke cewa mama kune tafe da ranan nan haka lafiya dai ko ga ku da kwandon goro, mana, Marya wace take saye da hijabin ta har kasa saidai fuskan ta ya koma wani dan fayau , da shi, Har kasa takai tagaida su daya bayan daya,, A hankali ta mike tsaye daniyar barin falon don bata san ko may yakawo su ba, Muryan baba yaji yana ce mata ta dakata, kada ta tafi tukun, Komawa tayi gurin da ta tashi takara dan zaunawa a wanan karon, Saidai atakure take gaban ta nadan faduw kadan kadan, Ungo nan maryam inji mijin mahaifiyar ta wanda ke gefen baba sam maryam bata san cewa dashi akazo ba sai yanzu, Da sauri tadago kai don taga ko may ye yake cewa wai ta karba, Kudine amma acikin envelop suke dan nawan karba tayi kamar yadda ya umurce ta da ta karba wai,, A hankali takai hannun ta takarbi kudin babane yai gyaran murya yana cewa Alhamdullahi, Maryam maryam din jin ankira sunan ta tadan dago kanta ta kalle shi a hankali, Ya ce karbi wanan rike tukun, Ta mika hannu a hankali ta karbi kudin hannun mahaifin ta, Yace to madallah ina Dije anty tace na,am baba yace Sadakin maryam ne nan na mika mata, Daga maryam har Anty dije cikin wani irin tashin hankali hankali suke kallon baba, din, Ba dai kr azaune ya na gyada kai, yace kwarai kuwa don dazun nan aka daura wa maryam din aure da yaron nan,,, Dammm gaban maryam din ya harba a lokaci guda dakin taga yana juya mata a lokaci guda kunnuwan ta yai mata wani kara tsuuuuu daga haka bata kara sanin inda take ba, Da,sauri Anty da kishiryar maman ta sukayo kanta , Ruwa masu sanyi a ka watsa mata, ajikin ta har zuwa kan ya hankan yasa ta sauke wani irin ajiyan zuciya mai karfi, Da sauri ts bude idon ta da suke a rufe tana tambayar baba ni bani maryam ka daurawa aure, Anty tace mata cikin kulawa, maryam kwantar da hankalin ki don baba ya tafi, Hannun Anty din maryam takamo tana cewa, Anty mafarki nakeyi ko, ? Ya baba zai mun haka anty komai nawa daban baba ke mun, Da sauri anty dije ta kwabe mata baki tana cewa, Baki da hankali ko kuwa babane kike nufin cewa bai son ki ko kuwa, Kuka wi, wi, wi maryam tasa a lokacin ta kwanta bisa kafadan anty Duk da Anty najin kukan har kasan zuciyar ta amma sai ta kyale maryam din a jikin ta koda hakan zai iya sa taji dan relief, Mahaifin Jibrin dattijon, yar shi ta,bashi shawaran daya kira don yaji ko may ke gudana, A hankali Yusuf ya jawo wayan shi don ya kira, dattijon,, Sai da yatabbatar da cewa yanzu dattijon ya dawo gida da ga massalaci, Mahaifin jibrin din yana zaune ya jawo tiren abincin shi a gaban shi don yaci, Hannun shi ya fara wanke yayin da kiran Yusuf ya shigo wayan nashi, Cikin sauri mahaifin Jibrin din ya dauko waya, ya karba kiran, Gaisawa suka fara yi a cikin mutunci nan yake tambayar Yusuf ko yana ina me yanzu, Yusuf din yabashi ansa da cewa yana Lagos ne ai , Tau inji mahaifin jibrin din wanda ke kokarin bude kulan abincin dake gaban shi, Kamshin mashanu ya na tashi wanda yasa dattijo dan lumshe idon shi,. Yaushe zaka dawo inji mahaifin jibrin din Yusuf ya ba shi ansa da cewa Sai nan da kwanaki don yazo yin wasu aiyukane idan yagama zai shigo, A zaton shi dattijon zai mai bayani akancewa ga yadda maganan take , Amma sai kawai yaji yana mashi fatan Alheri a rayuwa tare da fatan gamawa lafiya, ZEEE MAKAWA YALWA [4/28, 5:40 PM] ‪+234 902 951 1701‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Barka da jumma,a yan uwa Allah ya sada mu da alherin dake cikin wanan ranan,,,,,,,,,, RAMADAN KAREEM👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Kwance yake saman tafkeken gadon shi mai cin kusan mutun biyar, Barci yake son yi saboda jikin shi akwai a gajiya, amma yakasa saboda tunanen da yasha mai gaba, Kara juyawa yayi ko zai samu barcin yazo mai amma ina yakasa Mikewa yayi daga kwanciyar dayake ya sauko da kafafuwan shi kasa a hankali, Anty Dije ce ta fado mai arai agurin ta zai samu amsar damuwar shi, Kan shi yadaga a hankali ya kalli agogon dakin goma saura nadare don haka baya son ya takura mata, Balle ma matar aure ce duk kiran da zai mata da ranane ko kuma idan tana da magana itace kan kirashi da dare, Gurin window dakin ya nufa inda ya yaye labule ya zuge glass din a hankali, Wani irin fresh air ne ya shigo dakin a lokacin maidadi ya bude hancin shi ya shaki iskan ya dan lumshe idon shi, Ya dan kai wani lokaci agurin tsaye yana kallon yan motocin dake wucewa a titin jefi,jefi, Tsayin mintoci yana tsaye a gurin har na,wani lokaci sai kuma ya maida window yarufe kamar yadda yake da farko, Bathroom ya shiga inda watsa ruwa da kuma dauro alwala, don yai sallah nafila kafin ya kwanta, Wanan nafilan da yayi yasa shi samun relief mai sosai Don yayi barci mai nauyi har da mafarkin wata,zukekiyar yarinya tana shayar dashi wani abu mai dadi a cikin cup din tankagaram mai daukan ido, A daidai lokacin da yake kokarin dago kan shi ya kallo fuskan yarinyar sai kawai yaji wayar shi tana kuka acikin daren, Cikin jin haushin wanda duk ya katse mai wanan mafarki mai dadi da shiga rai da yake yi, ya farka, Hannu ya mika daidai gurin da wayan shi ke caji ya dauko wayar acikin kasala don duk jikin shi a mace yake jin shi, Samuel ne ke kiran shi da sauri ya duba time karfe biyu da wani abu na dare, Cikin sauri ya mustsike idon shi, babu abin da ya fado mai a rai kamar Dady shi, Don har gobe yana mutuwar son mahaifin shi a rayuwar shi, Fatan shi Allah ya nufi dad din shi da musulunta a rayuwar, shi, Yana daukar wayan muryan Samuel din ne cikin daga murya yake cewa, Brother Dad baia lafiya tunda rana yadawo daga filling station, Yana kiran sunan ka yana cewa ,Na, lie, Joseph no, go, marry, just like that, yana ta shan giya, ko na karbe, sai ya ansa ya sha,, Yanzu dai gashi har ta kai, jikin shi duk ya sake bai masan inda yake ba ga jikin tsufa, Yusu ya ji wani irin zafin jin wanan mugun labarin a zuciyar shi, Don haka ya rintse idon shi saboda takaici sai a yau yakara godewa Allah akan kwato shi da Allah yayi daga cikin kafirci, Amma a fili cewa Samuel yayi zai turo likita ya duba mahaifin nasu, Daga haka suka kashe wayen zuciyar bakikirin da jin wanan labarin takaicin da yayi, Barcin da bai koma ba ke nan saboda wanan mugun labarin mai takaici da Samuel ya sanar dashi, Yasan cewa ire iren wa yan nan dabi, un kesa wasu mutane suna masu gori masu karancin imani,,,,,, A hankali ta sako daga kan gadon ta,, ta na kokarin taka, kasa, amma tankar ansa ta takawa dole ne saboda irin yadda take jin tafin kafar ta yai mata nauyi, Toilet ta fada ta watsa ruwa saboda nauyin da take jin jikin ta yai mata, Daga haka ta dauro awala tazo zuwa gabatar da sallah, Bayan idar da sallah takai wani lokaci, a gurin zaune a takure, sai ta baka tausayi, Wani tunane ya a zuciyar ta, nan da nan gaban ta ya fadi tawani runtse idanun ta, Yanzu ita ya zata iya rayuwa da Yusuf a. matsayin mijin ta Wani irin taji a zuciyar ta. Inda ta runtse idon ta cikin jin kunan a zuciyar ta, Ita da wani ido zata kalle shi wai mijin ta yau, ita ya zata zauna da shi a matsayin zaman rayuwar aure, Ita ya zatai zama da yan uwan Yusuf kafirai arna a matsayin yan uwan miji dangin miji, Ya kuma zata kwashe da yan matan shi da tun ba,a kai ko ina ba har sun fara kai mata hari, Hawayen da ya taru tun farko a idon nata sune suka samu hanyar sulalowa, Bayan hannun ta tasa ta dan share hawayen a hankali, Dago kan da zatayi sai sukayi ido biyu da Anty ta wace ke tsaye tana kallon ta, cikin daure fuska, Inda take zaune tanufa ta samu saman stol din gado dake gefe ta zauna cikin damuwa , Maryam ban san may zan fada maki ba wanda zai sa ki yarda ki daina wanan halin, Maryam tadago indon ta da sukai jajajir tace dagani taci kuka, har ta gaji, Idan zakiyi hakkuri kiyi maryam kiroki Allah yasa hakan yafi zama maki alheri, Amma ba ki zauna kina ta rusa kuka har ki jawa kanki matsalar rayuwa, Still hannun ta ta kara sawa tagoge fuskan ta da yakoma kamar kamfanin fanfo, Saman jikin anty ta fada tana ta rusan kuka har sai da tasa duk daurewan Anty itama saida tai kukan, Ya illiya mijin Anty Dije ya katse masu kukan inda ya kira wayan yana tambayar matar yadda abubuwa ke guda na, Daga karshe yace abashi maryam din yana da magana da ita, Yace maryam ta ansa da naam cikin muryan kuka wanda yasa har saida yaji wani irin tausayin ta yakama shi, Maryam bana son wanan kukan da kikeyi pls, ki saurareni da kyau ki kwantar da hankalin ki, kiji abinda zan fada maki, Don dole badon taso ba tai shiru tana sauraren abinda mijin yar nata ke ce mata, Sai kai take kadawa alamar to ya cigaba da mata nasiha,, Nasiha masu ratsa jigi ya ya iliyan yai mata wanda don dole badon taso ba tai shiru, saboda maganganun sun bi jikin ta, Sosai maganar shi tasa maryam dan sakewa don daren ranan har taci abinci kadan, Sai dai rashin kuzarin da bata dashi don ta kasa sake jikin ta, Safiya ce ta fado mata a rai don duk wanan tashin hankalin da take ciki alamu ya nuna safiya din bata da labari akai, Kira guda gana biyu ta dauki wayan tana cewa yar halas kin ki ambato yanzu umma ke tambayar kwana biyu wai baki shigo ba, Jin shiru yasa safiya din cewa hello, muryan maryam kawai ya tabbatar mata ba lafiya, Cikin kuka maryam tace Safiya baba yadaura min aure yau, What inji Safiya tace wa maryam cikin daga sautin tambayam ta, Shehekan kukan da taji maryam din nayi ya tabbatar ma da maganar gaskiya maryam din ke yi, Duk da dare ya soma a lokacin hakan bai hana Safiya neman izini gurin mahaifiyar ta ba, Kwatsa sai ganin ta sukayi tayi sallama, a gidan Lokacin maryam wace ta dunkule a cikin bargo saboda sanyin da takeji ga ruwan sama an lema agarin,wuri ya dauki sanyi, Anty ce take mamakin ganin safiya ciki dare saboda bata saba,zuwa a wanan lokacin ba, Amma kuma sai ta nasa cewa ai kila safiya din ta samu labarin abinda ya faru da aminiyar ta, Bayan sun gaisa ne Anty dije din tace wa safiya sai kikaji labari kwatsam ko, Ki shiga tana ciki ai don haka safiya, ta shige dakin su maryam din cikin damuwa, Ganin yadda yaga maryam din a kwance yasa ta karasa gurin ta da,sauri tadan dafa goshin kan ta, Sai a lokacin maryam din ta bude idon ta ganin safiya ce yasa ta,saurin rungumota zuwa jikin ta, Nan suka dan yi kukan su suka,share hawayen su saboda kukan bashine mafita ba, Tun da gari yawaye yake ta faman aiwatar da,duk wasu abubuwan da yake da bukatan yi don ya samu ya koma Abuja , Abinda yafi bashi mamaki shine rashin kiran shi da,su KB basu yi duk cikin wanan lokacin shima dai share su yayi ya kama abinda ke agaban shi, Jirgn yamma yabi zuwa Abuja don haka acikin dare ya isa Abuja, Driver shi yazo yadauke shi zuwa gida duk da agajiye ya ke bai hana shi daga waya ya kira mahaifin shi ba, Don yaji lafiyan jikjn shi saboda yakira kafin ya taso akace yana barci ai, Yanzu da yakira bayan shigan shi gida ko daki bai shiga ba yakira don yaji, Inda yai sa,a ance yana zaune don haka aka bashi waya don su gaisa da mahaifin na shi, Maganar farko da Mr Emanuel yayi shi ne, Joseph are you married with a hausa girl,? Daddy just relax iam coming home tomorrow insha Allah, Jin haka yasa Mr Emanuel's saurin kashe wayan, Yusuf wanda yadda mahaifin nashi yai mai ya san cewa a kwai magana agaba, Saidai yana mai rokon Allah akan duk abinda zai faru Allah yakawo mai sauki, Daga haka ya haura zuwa sama don ya watsa ma jikin shi ruwa huta, Daga haka bai kara saukowa kasa ba don yana bukatan hutawa a tare da shi, Tunda safe babane ke sallama akofan gida jin muryan shi yasa kowa dake gidan tsinkewa saboda, ansa da akwai abinda ya kawo shi, Daguda guda suka dinga fitowa har Safiya din wace ta kwana gidan don taya aminiyar ta jamame, Sun gashe shi a cikin mutunci da kuma girmamawa irin yadda diya kewa iyayen su, Baba wanda yake tsaye daga kofan shigowa yadan jim Can ya kalli inda maryam take tsugune cikin zumbulelen hijabi, yace, Maryam , maryam wace jin an kara kiran sunan ta yauma din tadago takai kallonta gare shi a cikin girmamawa tace Na,am Baba, Yace Allah yai maki albarka kin ji Allah ya sa wa auren ki Albarka , Sai kuma yai shiru can yace ina Dije ? Anty Dije takarba dacewa Na,am baba Baba yace ban so ance jiya wanan yarinyar ta kwana gidan nan ba naso ace ta kwana adakin mijin ta, Gaba dayan su suka dago kai suna kallon mahaifin nasu, Yace na tuntubi shi malam mudi yace min abari har yaron yazo gari a ji ta bakin shi, Don haka sai ki zauna da shirin yar uwar taki akan duk ranan da mijin ta yazo zata tare a dakin ta ne Dafatan kin fahinci abinda nake nufi akan zance na, Anty Dije ta gyada kan ta tare da cewa eh baba shiru yadan yi yana kallon su yace Allah yai maku albarka Allah yabaku zuri,a masu albarka, Daga haka yasa kai zai wuce, sai kuma ya juyo gurin da Anty Dije take yadan juya yace bani son samun wani matsala, Anjima zandawo don muyi maganar dan abinda za,a sai mata, Sai a lokacin Anty Dije ta samu bakin magana tun shigowar baba gidan, Tace to amma baba bisa ga hukuncin da naji ka yanke na cewa da yazo ranan zata tare , Sai naga cewa ba,a fa yi wani shiri ba akan tarewan Don may baza a dan dakata harzuwa lokacin da za a shirya, Ke inji baba cikjn muryan da har saida ta dan razana yace, Ni komai nawa na dogora ga Allah wani shirine can, Abinda Allah ya hore min shi zamu kai mata tayi hakkuri yadda kowa yayi, Ina fatan kun fahinta da magana na don kadaazo ace min ga kara ka itace, Daga haka yasa kai ya wuce nan ya barsu a cikin tashin hankali, Daki maryam ta fada sai kawai ta ji hawaye ya na silalo, mata daga idon ta saboda hukuncin da baba ya yanke a kan ta, A daki maryam ce da aminiyar ta tana bata shawara akan tayi hakkuri da kaddaran ta, Shawarwari da dama Safiya din ta dinga ba maryan har taji hankalinta ya dan kwanta, Ànty Dije tun da tashirya tafita zuwa gidan wata aminiyar ta da suke siri Duk da matar ta girmay ta sosai sai amma suna siri da mutunci a tsakanin su, Saida taima matar bayanin abinda baba yazo masu da shi yau da safe, Na akan lalai sai dai maryam ta tare duk randa mijin ta yazo garin, Matar tai dariya tace wa dije wanan ai baika na ta da hankali ba, Don haka yanzu zan dan fita in je in fara samo hakki bakin daji, Anty Dije tace kai haba ke da anyi zance saiki maganar akan zancen gyaran harka, Nizancen abinda zan wa maryam na gyaran gida da dakina ke magana, Kai, matar ta kada tace aikin banza Dije, ai wanan abin shine babban tsaraba da yadace mugyara yafi wanan kayan banzan da kike zance, Saboda ai shi kayan daki babu inda sunna yace an halattawa mutun shi ko ? ZEEE MAKAWA YALWA [5/3, 10:46 AM] ‪+234 706 262 3470‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Barka da jumma,a yan uwa Allah ya sada mu da alherin dake cikin wanan ranan,,,,,,,,,, RAMADAN KAREEM👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Kwance yake saman tafkeken gadon shi mai cin kusan mutun biyar, Barci yake son yi saboda jikin shi akwai a gajiya, amma yakasa saboda tunanen da yasha mai gaba, Kara juyawa yayi ko zai samu barcin yazo mai amma ina yakasa Mikewa yayi daga kwanciyar dayake ya sauko da kafafuwan shi kasa a hankali, Anty Dije ce ta fado mai arai agurin ta zai samu amsar damuwar shi, Kan shi yadaga a hankali ya kalli agogon dakin goma saura nadare don haka baya son ya takura mata, Balle ma matar aure ce duk kiran da zai mata da ranane ko kuma idan tana da magana itace kan kirashi da dare, Gurin window dakin ya nufa inda ya yaye labule ya zuge glass din a hankali, Wani irin fresh air ne ya shigo dakin a lokacin maidadi ya bude hancin shi ya shaki iskan ya dan lumshe idon shi, Ya dan kai wani lokaci agurin tsaye yana kallon yan motocin dake wucewa a titin jefi,jefi, Tsayin mintoci yana tsaye a gurin har na,wani lokaci sai kuma ya maida window yarufe kamar yadda yake da farko, Bathroom ya shiga inda watsa ruwa da kuma dauro alwala, don yai sallah nafila kafin ya kwanta, Wanan nafilan da yayi yasa shi samun relief mai sosai Don yayi barci mai nauyi har da mafarkin wata,zukekiyar yarinya tana shayar dashi wani abu mai dadi a cikin cup din tankagaram mai daukan ido, A daidai lokacin da yake kokarin dago kan shi ya kallo fuskan yarinyar sai kawai yaji wayar shi tana kuka acikin daren, Cikin jin haushin wanda duk ya katse mai wanan mafarki mai dadi da shiga rai da yake yi, ya farka, Hannu ya mika daidai gurin da wayan shi ke caji ya dauko wayar acikin kasala don duk jikin shi a mace yake jin shi, Samuel ne ke kiran shi da sauri ya duba time karfe biyu da wani abu na dare, Cikin sauri ya mustsike idon shi, babu abin da ya fado mai a rai kamar Dady shi, Don har gobe yana mutuwar son mahaifin shi a rayuwar shi, Fatan shi Allah ya nufi dad din shi da musulunta a rayuwar, shi, Yana daukar wayan muryan Samuel din ne cikin daga murya yake cewa, Brother Dad baia lafiya tunda rana yadawo daga filling station, Yana kiran sunan ka yana cewa ,Na, lie, Joseph no, go, marry, just like that, yana ta shan giya, ko na karbe, sai ya ansa ya sha,, Yanzu dai gashi har ta kai, jikin shi duk ya sake bai masan inda yake ba ga jikin tsufa, Yusu ya ji wani irin zafin jin wanan mugun labarin a zuciyar shi, Don haka ya rintse idon shi saboda takaici sai a yau yakara godewa Allah akan kwato shi da Allah yayi daga cikin kafirci, Amma a fili cewa Samuel yayi zai turo likita ya duba mahaifin nasu, Daga haka suka kashe wayen zuciyar bakikirin da jin wanan labarin takaicin da yayi, Barcin da bai koma ba ke nan saboda wanan mugun labarin mai takaici da Samuel ya sanar dashi, Yasan cewa ire iren wa yan nan dabi, un kesa wasu mutane suna masu gori masu karancin imani,,,,,, A hankali ta sako daga kan gadon ta,, ta na kokarin taka, kasa, amma tankar ansa ta takawa dole ne saboda irin yadda take jin tafin kafar ta yai mata nauyi, Toilet ta fada ta watsa ruwa saboda nauyin da take jin jikin ta yai mata, Daga haka ta dauro awala tazo zuwa gabatar da sallah, Bayan idar da sallah takai wani lokaci, a gurin zaune a takure, sai ta baka tausayi, Wani tunane ya a zuciyar ta, nan da nan gaban ta ya fadi tawani runtse idanun ta, Yanzu ita ya zata iya rayuwa da Yusuf a. matsayin mijin ta Wani irin taji a zuciyar ta. Inda ta runtse idon ta cikin jin kunan a zuciyar ta, Ita da wani ido zata kalle shi wai mijin ta yau, ita ya zata zauna da shi a matsayin zaman rayuwar aure, Ita ya zatai zama da yan uwan Yusuf kafirai arna a matsayin yan uwan miji dangin miji, Ya kuma zata kwashe da yan matan shi da tun ba,a kai ko ina ba har sun fara kai mata hari, Hawayen da ya taru tun farko a idon nata sune suka samu hanyar sulalowa, Bayan hannun ta tasa ta dan share hawayen a hankali, Dago kan da zatayi sai sukayi ido biyu da Anty ta wace ke tsaye tana kallon ta, cikin daure fuska, Inda take zaune tanufa ta samu saman stol din gado dake gefe ta zauna cikin damuwa , Maryam ban san may zan fada maki ba wanda zai sa ki yarda ki daina wanan halin, Maryam tadago indon ta da sukai jajajir tace dagani taci kuka, har ta gaji, Idan zakiyi hakkuri kiyi maryam kiroki Allah yasa hakan yafi zama maki alheri, Amma ba ki zauna kina ta rusa kuka har ki jawa kanki matsalar rayuwa, Still hannun ta ta kara sawa tagoge fuskan ta da yakoma kamar kamfanin fanfo, Saman jikin anty ta fada tana ta rusan kuka har sai da tasa duk daurewan Anty itama saida tai kukan, Ya illiya mijin Anty Dije ya katse masu kukan inda ya kira wayan yana tambayar matar yadda abubuwa ke guda na, Daga karshe yace abashi maryam din yana da magana da ita, Yace maryam ta ansa da naam cikin muryan kuka wanda yasa har saida yaji wani irin tausayin ta yakama shi, Maryam bana son wanan kukan da kikeyi pls, ki saurareni da kyau ki kwantar da hankalin ki, kiji abinda zan fada maki, Don dole badon taso ba tai shiru tana sauraren abinda mijin yar nata ke ce mata, Sai kai take kadawa alamar to ya cigaba da mata nasiha,, Nasiha masu ratsa jigi ya ya iliyan yai mata wanda don dole badon taso ba tai shiru, saboda maganganun sun bi jikin ta, Sosai maganar shi tasa maryam dan sakewa don daren ranan har taci abinci kadan, Sai dai rashin kuzarin da bata dashi don ta kasa sake jikin ta, Safiya ce ta fado mata a rai don duk wanan tashin hankalin da take ciki alamu ya nuna safiya din bata da labari akai, Kira guda gana biyu ta dauki wayan tana cewa yar halas kin ki ambato yanzu umma ke tambayar kwana biyu wai baki shigo ba, Jin shiru yasa safiya din cewa hello, muryan maryam kawai ya tabbatar mata ba lafiya, Cikin kuka maryam tace Safiya baba yadaura min aure yau, What inji Safiya tace wa maryam cikin daga sautin tambayam ta, Shehekan kukan da taji maryam din nayi ya tabbatar ma da maganar gaskiya maryam din ke yi, Duk da dare ya soma a lokacin hakan bai hana Safiya neman izini gurin mahaifiyar ta ba, Kwatsa sai ganin ta sukayi tayi sallama, a gidan Lokacin maryam wace ta dunkule a cikin bargo saboda sanyin da takeji ga ruwan sama an lema agarin,wuri ya dauki sanyi, Anty ce take mamakin ganin safiya ciki dare saboda bata saba,zuwa a wanan lokacin ba, Amma kuma sai ta nasa cewa ai kila safiya din ta samu labarin abinda ya faru da aminiyar ta, Bayan sun gaisa ne Anty dije din tace wa safiya sai kikaji labari kwatsam ko, Ki shiga tana ciki ai don haka safiya, ta shige dakin su maryam din cikin damuwa, Ganin yadda yaga maryam din a kwance yasa ta karasa gurin ta da,sauri tadan dafa goshin kan ta, Sai a lokacin maryam din ta bude idon ta ganin safiya ce yasa ta,saurin rungumota zuwa jikin ta, Nan suka dan yi kukan su suka,share hawayen su saboda kukan bashine mafita ba, Tun da gari yawaye yake ta faman aiwatar da,duk wasu abubuwan da yake da bukatan yi don ya samu ya koma Abuja , Abinda yafi bashi mamaki shine rashin kiran shi da,su KB basu yi duk cikin wanan lokacin shima dai share su yayi ya kama abinda ke agaban shi, Jirgn yamma yabi zuwa Abuja don haka acikin dare ya isa Abuja, Driver shi yazo yadauke shi zuwa gida duk da agajiye ya ke bai hana shi daga waya ya kira mahaifin shi ba, Don yaji lafiyan jikjn shi saboda yakira kafin ya taso akace yana barci ai, Yanzu da yakira bayan shigan shi gida ko daki bai shiga ba yakira don yaji, Inda yai sa,a ance yana zaune don haka aka bashi waya don su gaisa da mahaifin na shi, Maganar farko da Mr Emanuel yayi shi ne, Joseph are you married with a hausa girl,? Daddy just relax iam coming home tomorrow insha Allah, Jin haka yasa Mr Emanuel's saurin kashe wayan, Yusuf wanda yadda mahaifin nashi yai mai ya san cewa a kwai magana agaba, Saidai yana mai rokon Allah akan duk abinda zai faru Allah yakawo mai sauki, Daga haka ya haura zuwa sama don ya watsa ma jikin shi ruwa huta, Daga haka bai kara saukowa kasa ba don yana bukatan hutawa a tare da shi, Tunda safe babane ke sallama akofan gida jin muryan shi yasa kowa dake gidan tsinkewa saboda, ansa da akwai abinda ya kawo shi, Daguda guda suka dinga fitowa har Safiya din wace ta kwana gidan don taya aminiyar ta jamame, Sun gashe shi a cikin mutunci da kuma girmamawa irin yadda diya kewa iyayen su, Baba wanda yake tsaye daga kofan shigowa yadan jim Can ya kalli inda maryam take tsugune cikin zumbulelen hijabi, yace, Maryam , maryam wace jin an kara kiran sunan ta yauma din tadago takai kallonta gare shi a cikin girmamawa tace Na,am Baba, Yace Allah yai maki albarka kin ji Allah ya sa wa auren ki Albarka , Sai kuma yai shiru can yace ina Dije ? Anty Dije takarba dacewa Na,am baba Baba yace ban so ance jiya wanan yarinyar ta kwana gidan nan ba naso ace ta kwana adakin mijin ta, Gaba dayan su suka dago kai suna kallon mahaifin nasu, Yace na tuntubi shi malam mudi yace min abari har yaron yazo gari a ji ta bakin shi, Don haka sai ki zauna da shirin yar uwar taki akan duk ranan da mijin ta yazo zata tare a dakin ta ne Dafatan kin fahinci abinda nake nufi akan zance na, Anty Dije ta gyada kan ta tare da cewa eh baba shiru yadan yi yana kallon su yace Allah yai maku albarka Allah yabaku zuri,a masu albarka, Daga haka yasa kai zai wuce, sai kuma ya juyo gurin da Anty Dije take yadan juya yace bani son samun wani matsala, Anjima zandawo don muyi maganar dan abinda za,a sai mata, Sai a lokacin Anty Dije ta samu bakin magana tun shigowar baba gidan, Tace to amma baba bisa ga hukuncin da naji ka yanke na cewa da yazo ranan zata tare , Sai naga cewa ba,a fa yi wani shiri ba akan tarewan Don may baza a dan dakata harzuwa lokacin da za a shirya, Ke inji baba cikjn muryan da har saida ta dan razana yace, Ni komai nawa na dogora ga Allah wani shirine can, Abinda Allah ya hore min shi zamu kai mata tayi hakkuri yadda kowa yayi, Ina fatan kun fahinta da magana na don kadaazo ace min ga kara ka itace, Daga haka yasa kai ya wuce nan ya barsu a cikin tashin hankali, Daki maryam ta fada sai kawai ta ji hawaye ya na silalo, mata daga idon ta saboda hukuncin da baba ya yanke a kan ta, A daki maryam ce da aminiyar ta tana bata shawara akan tayi hakkuri da kaddaran ta, Shawarwari da dama Safiya din ta dinga ba maryan har taji hankalinta ya dan kwanta, Ànty Dije tun da tashirya tafita zuwa gidan wata aminiyar ta da suke siri Duk da matar ta girmay ta sosai sai amma suna siri da mutunci a tsakanin su, Saida taima matar bayanin abinda baba yazo masu da shi yau da safe, Na akan lalai sai dai maryam ta tare duk randa mijin ta yazo garin, Matar tai dariya tace wa dije wanan ai baika na ta da hankali ba, Don haka yanzu zan dan fita in je in fara samo hakki bakin daji, Anty Dije tace kai haba ke da anyi zance saiki maganar akan zancen gyaran harka, Nizancen abinda zan wa maryam na gyaran gida da dakina ke magana, Kai, matar ta kada tace aikin banza Dije, ai wanan abin shine babban tsaraba da yadace mugyara yafi wanan kayan banzan da kike zance, Saboda ai shi kayan daki babu inda sunna yace an halattawa mutun shi ko ? ZEEE MAKAWA YALWA [5/3, 10:49 AM] ‪+234 706 262 3470‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Bazan iya matawa da ku ba masoya wanan novel din kaunar da shi tankar a gare ni ne nagode nagode nagode Allah yakara rufa asiri a rayuwa,,,, Maryam wace take zaune tai tagumi da hannun ta guda, Kallon abinda uwale takawo mata acikin roba takeyi, Gashi uwale tace sai ta shanye shi duk gaba daya, yau din nan, Safiyace ta shigo dakin inda idon ta ya hango mata abin kamar yadda aka ba ta, Isa tayi gurin inda ta jawo wani cup dake gefe, ta debo wanan gumbar ta sa aciki, Bayan ta gama damawa ta dauko madaran peak milk gwagwani guda ta juye a ciki, Cikin tamke fuska tamikawa maryam din wace ke zaune a gefe guda, Maryam da bata da wani option sai na ta karba ahaka takarbi cup din a hannun safiya ta fara kurban a hankali tana dan runtse idon ta, Wani ruwa maikama da ruwan lalai yana kamshin turare a cikin shi safiya takaiwa maryam din a bathroom, A ranan kusan sau biyar maryam tai wanka da wanan ruwan hadin ga kuma yakin jiki da safiya din da Anty ke tsare ta sai tayi wa jikin ta, Jikin ta a cikin kwana guda ya sauya kalla, duk da ta ramay amma sai jikin nata yai wani fresh, Ruwan kanin fari watau, (glove) cike a wani roba mai marfi shi ma tadinga shan shi, tare da yin tsarki da shi a wanan yinin, Anty Dije da kanta sai da taga canji a gurin yar kaunar nata, Takoma wata fresh sai sheki takeyi jikin ta ya sauya a lokaci guda, Kwana biyu ga naman yan shilan tantabara da uwale ke daho mata daga gidan ta ace wai ita kadaice zata zauna ta cinye, kashi kawai zata bari, Abubuwa kala,kala aka dinga yiwa maryam din wanda ya kawo mata sauyi, a jikin ta, ita kanta har muryan ta duk taji ya sauya mata ga wani irin kasala wanda ke sata, barci a kai,kai, ,,,,, Shiri yayi so sai don yasan cewa wanan tafiyan ya na bukatan kudi, Gashi kuma mai laifi a gurin jama,a da dama bai san yadda zai wanke kanshi ba musan ma yar uwar shi dayake ji da ita Anty dije Wace rabon da suyi waya da ita tun yana garin kano har zuwa yau bai kara kiran ta ba, Saboda aiyukan da suka sha mai kai gashi kuma wani sabon magana ya bullo wanda yasan cewa zancen yakai gare ta a yanzu, Sai kuma mahaifin shi wanda har zancen takaishi ga kwantawa ciwo sai rokon Allah yakeyi, akan Allah yasa ya samu kan mahaifin nashi ,, Gudu motocin keyi kamar yadda suka saba yi a daji amma shi yau bashi ke tuki ba yazo da mutanen shi don haka, suke jan mota, Sai lokacin da motar ta doshi garin kamfanin bobi sanan maryam tafadowa Yusuf a rai, Maryam ya furta a hankali tare da lumshe idon shi da su kayi ma jajir a lokacin saboda stress, da yai mai yawa, Idon shi ya lumshe a lokacin tare da tunanen abinda ya yanke a tsakanin shi da maryamm din, Sonny kawai yakai mai can a irin yadda yake jin maryam a rayuwar saboda Yarinya tayi mai a irin yadda yake son mace,, Komawa yayi yabi lafiyan kujeran motan yana mai lunshe idon shi gami da shafo fuskan shi, Ba,a dauki wani lokaci mai tsawo ba suka shiga garin kwantagora, Direct gidan shi suka fara zuwa inda suka dan huta, tukun tare da kokarin neman abinda sukaci,, Amma banda Yusuf wanda ke jin shi a koshe lokacin baya bukatan cin komai a rayuwar shi, Driver shi guda wanda yasan gidan su Anty Dije ya umarta da yakai masu tsaraban su kamar yadda ya saba kai masu, Shi kuma yadauki mota shi kadai yabar gidan ba tare da kowani execute ba, Gidan mahaifin shi ya nufa kai tsaye ba tare da wani shakkan komai ba,,,,, Zaune suke a falon su gaba dayan su maryam wace ke rike da wani fresh milk na shanu da uwale takawo mata shi wai ta shanye dukka, Sallaman da sukaji ne na wani mutun inda, Assalam ya,sheka waje don ya,diba masu kowa ke sallama a lokacin, Sai gashi da gudun shi yana cewa uncle din shi ya, uncle din shi yazo sai kuma sukaji karan ana,sauke kaya a tsakar gida, Ba maryam ba har su Anty sai da ga ban su ya fadi , badon komai sai don tunawa,da alkawarin baba na,cewa,duk ranan da Yusuf ya,shigo gari a, ranan maryam zata tare a dakin ta,, Cup din dake a hannun tane ya ke batun faduwa wanda,safiya tai saurin karban cup din,, Mikewa,tayi zuwa,dakin su cikin tashin hankali don jikin ta har rawa yake yi, a lokacin, Sadiya ce ta mara mata baya ganin irin yanayin da aminiyar nata take ciki, Dafa, mata kafadar ta Safiya tayi tana mai kallon ta, Maryam ta,dago kan ta a hankali tana kallon safiya din, Idon ta na silalan hawaye kai safiya ta girgiza mata ta bude baki cikin kariyan murya ta ce, Ka dakiyi haka pls ki zama mai dauri ga duk jarrabawan da kika gani ga rayuwan ki, Cikin muryan kuka maryam tacewa safiya amma dai kin ji abinda baba yace ko, ? Kan,ta ta girgiza cikin kuka tace, wa maryam din ai ba lalai bane maganar baba din yayi tasiri a yau din don shima ai yana da nashi uzurin ko, Sai a lokacin hankali maryam ya dan kwanta a haka tadan kai kwance ta dunkule guri guda kamar wace ki jin sanyi, Zuciyar ta fam da tunane da addu,a Allah yasa maganar safiya ya zamo gaskiya, Bayan ya kashe mota yafito yana rike da yar jakar gift da ya sayowa, mahaifin nashi, a lokacin, Tundaga kafan shi har kai kallo daya zakai mai kasan cewa Naira ta yi rana agurin, Tafiyan shi cikin takon kasaita irin na gogaggun matasan yan Abuja ko lagos, Dan sajen da ya bari wanda yai mai round a fuska yakara fitar mai da kyaun fuskan shi fili, Duk yadda matasan da ke gidan nasu suna kula da aiyukan gida , Sunzo karban ledar dake hannun shi amma sam ya hana ya na mai daga masu hannu alamar subar shi kawai,, A sama resting chair yasamu Dad din shi ya dan kishingida kamar mai tunane muryan Yusuf yaji daga sama don sam bai tsanmani zuwan shi ba yanzu, Direct gurin shi ya nufa, nufa yadan rungumo Dad din zuwa jikin shi, Cikin lumshe idanun shi yace ma dan nashi you are welcome my child, Tare da dan bubuga mai bayan shi cikin nuna mai kulawan ganin shi, Kujera dake facing din inda Dad din yake ya nufa nan ya zauna suna facing din juna yadan tura mai ledan gift din da yazo mai da su, Babu wanda keda alaka da giya ko wani abin maye daga duk cikin kwalaben, drinks din na karin jini ne da gyaran jiki, A hankali tsohon yadago kai ya kallo dan nashi daga inda yake ya ce, Joseph da gaskiyane ka auri yarinyar hausawa, kokuwa kana shirin aura ne, Ba wani tsoro ko fargaba Yusuf din yace, baba da ba hausa da yar IBO duk guda ce fata dai in samu wace hankalin mu yazo daya, Hannu Mr Emanuel yadaga wa Yusuf din wanda ya fara yiwa mahaifin shi dogon sharfi, Dan tsohon yace lalai Yusuf yanzu kan nagane cewa kafita cikin mu gaba daya, Don har gudun auren yar kabila, ka kake yi, yan mata nawa aka kawo min cewa in aura maka amma nace a,a don ina da, ra,ayinka zabi mace da kan ka, Shiru yayi saboda wani irin bakin ciki da ya taso mai har yaji cewa bazai iya ci gaba da zancen ba, Shima Yusuf din baiji dadi ba sam irin yadda ya ga rayuwar mahaifin nashi ya baci, Sun yi shiru nawa ni lokaci don haka Yusuf din ya mike saboda yana da bukatan zuwa gurin mahaifi Jibrin don karin bayani, Acikin rashin sa,a Yusuf bai samu mahaifin jibrin din a gida ba don haka ya juya motar shi sai zuwa gidan Anty dije, Yasan cewa yau zai sha fadan rashi kiran su da baiyi ba kwana biyu kuma layin da zasu iya samun shi duk a rufe suke, Da sallaman shi ya shigo gidan wanda kamshin shi kawai ya isarwa mutun sakon cewa yana a gurin, Waje suke a zaune saboda garin akwai hadari wanda ke yawo a sararin samaniya tun da rana Yanzu kuma sai yadan ba garin zafi,zafi da dan lumshi,lumshi, Masara ce gassasa a ga ban su suke ci yayin da anty take kokarin hada kaya a cikin kitchen, saboda ganin hadarin da tayi, Ganin shi girshi da sukayi babu wani hanya da zai sa maryam din ta boye mai, Kallo guda su kai wa juna daga ita har shi kowan su ya kauda kai ga dan uwa, Kowa da abinda yake sakawa azuciyar shi don ganin dan uwa da sukayi, Safiya ce da Anty ke mai sannu da zuwa a lokacin sai maryam wace ke ta baya kadan ta mai sannu da zuwan acikin wani irin murya mai karyarwa, a,ciki, ciki, May yasa may ta ta ramay haka ? Amma kuma ga jikin ta yai wani fresh maryam din yaga duk ta canza a lokaci guda, Ita kuma maryam Yusuf din ne taga yakoma mata wani iri tankar yaune ta fara ganin shi, A galon su , suke zaune suna gaisawa da Anty Dije wace bata san ko may yasa ba yau kawai ta tsinci kan ta da jin kunyan kanin nata, haka kawai, Ya dan dago kai yana mata dan murmushin nan tashi ta bajin ta, Anty Dije wace ala dole take wanan zaman da Yusuf din Cikin dan dukar da kai tace wa Yusuf din, cikin marai,rai ce war murya, Yusuf kawai sai kaji yadda zance ya kasan ce daga karshe ko, Baba ya ya yiwa kowa baza ta don ko ni ban san da zancen auren nan ba sai bayan anyi, Kasan irin yadda maryam din tai ta fama da jin jiki, Duk wanan bayanin bata lura da cewa kallon mamaki Yusuf din ke mata a lokacin. Anty ban fahinci maganar ki ba inji Yusuf din yake tabayar anty dijen, Anty ta kara cewa nasan saboda mugun ciwon kan nan da tayi ya firgita ta shi, Irin yadda maryam ta firgice ai duk wanda ya gan ta sai ya ji tsoro a lokacin, Maryam din tayi ciwo ne har haka anty ya tambaya a cikin kulawa, Nan anty ta kwashe duk yadda abin ya kasan ce ta,bashi labari, har zuwa zancen daurin auren su, Cikin tambayar da ta gigitashi yace Anty kina nufin cewa maryam a matsayin mata ta take yanzu nan, Mamakin tambayar da Yusuf yai mata taji saboda tazaci cewa tun farko ya san da zancen, Cikin mamaki Anty Dije tace kana nufin cewa, baka da labarin daurin Auren ku kaida maryam din, Hasbunallahi wani,imal wake,el,,, Sai kuma yai shiru inda yadaga kan shi ya na dan kallon saman silindin dakin bakin shi na motsi, kawai, Da alamar addu,a ya keyi a lokacin, don haka ido Anty dije tabishi da shi, Yakara dago kai tankar zaiyi magana amma kuma sai ya kasa,cewa komai yai shiru, Muryan Anty Dije ne yadawo dashi ga tunanen da ya fara inda yaji tana cewa, Gashi baba yai alkawarin cewa duk ranan da kazo a wanan ranan maryam zata tare a gidan ka, Cikin rashin fahintar may hakan da anty dije tace yake nufi , Ganin bai fahince ta ba yasa ta cewa maryam din baba yace a yau zata shiga gidan ka, Cikin sauri Yusuf ya tare ta da cewa haba haba anty, Kada baba ya ce haka pls Yabari har muyi styling pls, ? Murmushi Anty dije tayi ta dan kalle shi tace baka da inda zaka satane Yusuf ,? Anty amarya ai sai sabon gida ko kamai ma sabo ko Cikin mamaki anty dije tace ma Yusuf din , kai a ina kake zama ? Yace a wanan dan gidan nawa mana kinga ai ban yi shi as na mace ba ko ? Hmmm inji Anty Dije saboda mamaki abinda Yusuf yace a kan gidan da yake a ciki, Ganin tana mamakin yasa shi cewa a gaskiya ban dauka cewa auren mu da maryam zai zo da wuri ba haka don haka ne ma ban wani dade da sayen fili ba nasa ai mun irin plan din ginan da nake son inwa mata ta ta zauna a ciki, Sai kuma ya wani irin nisawa bayan yakai karshen maganar ta shi,,, Shiru sukayi gaba dayan su a lokaci guda, Kowa da irin abinda yake tunane a cikin zuciyar shi, Mikewa yayi saboda yatafi gurin mahaifin Jibrin din don yana son ganin shi sosai don jin karin bayani, Duk da zuciyar shi har gagan jikin shi rawa sukeyi a lokacin saboda duk a rude yake, Mamaki kawai yakeyi wai maryam ce yau a matsayin matar shi, Jin abin yakeyi tankar a mafarki, ba wai a fili ba, sai da ya kai kofar fita yadan cewa Anty Dije saida safe don da wuya yadawo anjima Murmushi tabi bayan shi da saboda ganin irin yadda ya rude a lokaci guda, Abin mamaki yana fita waje a gurin da yabar su maryam din a zaune ba su gurin daga ita har safiya din, Yaso kwarai ya kara ganin yarinyar saboda tausayin take bashi , Bai tsaya wani mamakin ina suke ba don yasan cewa saboda shi ne, suka boye, Gidan mahaifin Jibrin din yakoma, inda yaci sa,a wanan karon dattijon yana gida,, A cikin mutunci da nuna kulawa, dattijon yatari Yusuf din, Kamar yadda yaran hausawa suke gaida na gaba dasu Haka,Yusuf din ya durkusa har kasa ya gaida mahaifin jibrin din, Bayan sun gaisa, ne a cikin walwala, Dattijon ya tambaye shi, gajiyan tafiya,? Sai Yusuf din ke fadawa mahaifin na jibrin cewa yazo ai dazun bai samay shi a gida ba, Dattijon ya ce Allah sarki ai nadan zagaya nan bayan layin mune gaida wani makwabcina da yadawo umura, Yusuf yace shima yana da sha,awan bana ya tafi Umarh din nan insha Allah, Haka akeso ai, inji dattijon ya ce wa Yusuf din, Kullun ana son al,uman manzo S,A,W su bazama izuwa gurin ibada kasa mai tsarki, Saboda kara samun ci gaban musulunci a cikin duniya, Yakare da cewa Allah yasa, Musulunci ya rinjayi kafirci akoda yaushe, Yusuf ya karba mai da fadin amin, Ya Allah,,, Dan shirune ya biyo bayan hiran nasu a lokacin, ZEEE MAKAWA YALWA [5/3, 10:53 AM] ‪+234 706 262 3470‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣6⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA, YAURI RAMADDAM KAREEM👏👏👏👏👏👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Yusuf yana mai sunkuyar da kan shi a kasa , Sai shi daddtijon ne yai gyaran murya inda ya soma magana kamar haka, Yusuf, kasan cewa yanzu dai duk musulmi na kwarai yakan yadda da kaddara, Walau, mai kyau ko akasin ta watau mara kyau ke nan abin nufi, Yusuf din yace hakanane baba dattijon ya ansa da fadin da kyau dan Albarka, Yaci gaba da cewa ta a bayan ka abubuwa da dama sun faru. A nan ya zayyane masa yadda sukayi tun daga farko da mahaifin su maryam din har zuwa daurin aure, Kaga kenan al,amarin ubangiji ba, ai,mai shishigi, Shiru Yusuf din yayi a lokacin tankar bazai yi magana ba , Har dattijo ya zaci cewa ko bai yi naam da zancen auren bane, haka, Sai kuma yaga cewa ai Yusuf din ya can,canci ai mai wanan irin sakkayan da mahaifin su maryam yai mai, Don gaskiya Yusuf mutum mai taimako da kyautatawa na kasa da shi, Gashi ya fitar da jama,a da dama daga cikin kangin talauci kai taimakon shima dai mara adadine, Amma kuma sai gashi wai mutum butulu ana,son abin hannun shi amma baza a iya hada zuria, da shi ba kamar ba musulmi ba, To amma kuma gashi wanan bawan Allah yanuna halarcin shi gare shi, Ya nuwa duniya bai kwadayin abin shi sai dai fatan alheri, Don ko sadaki shi da kanshi ne ya matsa mai akan abarshi a dubu hamsin , Don shi mahaifin yarinyar yanuna, wai dubu ashirin ne, za,a bayar da farko, Muryan Yusuf din ce ta katse mai tunanen ida acikin murya irin ta mai zubbar da hawaye, yace wa dattijon, Baba ban da abin da zan furta a gare bayan ince Allah ya sa agama da duniya lafiya, A cikin sauri dattijon ya ansa da fadin amin amin ya na mai gyara zaman shi, Sai kuma yadan yi shiru hannun shi yasa ga aljihun shi yana kirgo kudin daga ciki, Yan dubu guda gudane sababbi fill da su ya aje a gaban baban nasu, Yace baba ga kudin da kuka bayar na sadiki sai kuma kudin goro da sauran su, Kai, kai, inji mahaifin Jibrin din ya ce wa Yusuf cikin dan ja da baya kusa da kudin da Yusuf din ya aje, kamar wani wanda yaga abin tsoro, Haba Yusuf ashe baka dauke ni a matsayin mahaifi ba, No, no ba haka na bane baba, don Allah kayi hakkuri ka fahince ni, Haba Yusuf duk abinda zan iya yi,wa Jibrin zan iya maka shi aduniyan nan , Sanan malam Abdulsamad shine ya siyo su goro da alawa, wanda aka rabawa mutanen, Da suka sheda daurin auren naka don dai alhamdullahi mutane da dama sun sheda wanan daurin auren na ku, so sai,,, Shirun da wurin ya dauka gaba daya shi ya sanya mahaifin Jibrin gane cewa Yusuf kuka yake, Haba Yusuf ka kara godewa Allah ka da ya kaddare ka da yin wanan auren, cikin mutunci da girmamawa, Don duk yadda ake halarci mahaifin Yarinyar ya yi gaskiya, saboda duk yadda yadace na gwada inda na fahinci cewa tsakani da Allah ya baka yar shi ba don kwadayin duniya ba, Yusuf yace wa mahaifin Jibrin din nasan da haka baba, Don wa yan nan mutane suna daga cikin sahun farko na tallafawa shi ga na, addini nan, Saboda sam basu kyamace ni ba a rayuwar su, a lokacin danake cikin batar kai, kamar yadda sauran mutane ke nuna min kyama a baya,, Kiran sallah da ya karade gari alamar magriba ya yi a lokacin shi dan tsaida zancen nasu, Don haka suka mike kusan lokaci guda don haramar dauro alwala, Amma sai Yusuf din ya dakatar da dattijon da cewa dazun na tafi gidan ita yar yarin wace ke rikon ta, Take sheda min cewa wai mahaifin nasu yace, duk ranan da nazo a ranan yariyar zata tare agida na,, Kai mahaifin Jibrin din ya kada yana cewa hmm malam Abdul zai iya yin fiye da hakan ai, Don shi mutum ne mai ra,ayin kan shi bai bin ra,ayi al,umma, To kai yanzu ya kake so a yi ne ? Kai yadan sosa alamar jin kunya, yace baba naso ne ai mata kamar yadda naga hausawa nawa yaran su a gurin aure don saboda hankalin yarinyar ya dan kwanta, Indan mun fito daga massallaci zan je gurin shi insha Allah, za a san yadda za,a yi, Anty Dije wace tun bayan tafiyan Yusuf din duk ta rude saboda sanin halin mahaifin su da tayi, cewa bai magana biyu a rayuwar shi, Don haka ta dauki waya kamar yadda ya umurce ta, da tayi a duk ranan da Yusuf ya shigo gari, Bayan sun gaisa ne anty ke sheda mai cewa Yusuf yana gari don har ma yazo gidan ta dazun nan, Albarka yadinga sa mata don bin umurnin shi da tayi ta sanar dashi a lokaci kamar yadda ya umurce ta din, Nan yace mata da zaran an fito daga massalaci zai zo gidan nasu amma kafin nan duk wani shiri da ya dace tai wa maryam din ta tabbatar da cewa tayi mata shi, Tun bayan kashe wayan su da babane sai Anty Dije taji idon ta ya ciciko da hawaye tausayin kaunar ta ya kamata, Gidan uwale ta shiga inda tai mata bayanin komai kamar yadda mahaifin nasu ya, umurce, ta da, tayi,, Don haka a,tare da Uwale Anty tashigo gidan a lokacin maryam da Safiya suna tare suna dan hiran su, Safiya ce ke kokarin jan maryam din da hira don ta kwantar mata da hankali kamar ba komai, Ganin shigowar su yadan tayar wa maryam da hankali amma da yake ita uwale irin wayyayun matan nan sai cewa tayi , Haba maryam may ye haka mijin ki na agari amma zaki zauna a haka ba wani gyara jiki, Ta juya gurin da Anty Dije take tana cewa haba Hadiza kina kallo ko wani gyara baki mata ba idan ya shigo ya samay ta a haka fa, Maza tashi ki gyara jikin ki kafin ya dawo ya samayki ba wani gyara, Maryam ta turo baki gaba saboda jin haushin maganar da Uwale tai mata na cewa wai mijin ta, Sai taji duk ta wani tsani Yusuf din kwatakwata arayuwar ta, Amma sai taji Anty na cewa tashi mana maryam ana magana da ke, Ba bata lokaci maryam ta mike inda uwale taimata nuni da cewa su je makewayi, Abubuwa na gyaran jiki ta umarci maryam din da tayi a bathroom din , Inda uwale ke ta wajen bayin tana umurtan maryam da cewa yi kaza sa kaza gyara kaza har ta kimtsa tafito, Wasu kayan kamshi ne aka bata tashafa wa jikin ta, inda duk hawaye ya cikawa maryam din ido a lokacin, Daga matse,matsin ta har zuwa cibiyanta sai da uwale tasa maryam din ta shafe shi da wani dan ruwan mai kamshi acikin wani dan kwalba, Daga haka kuma Safiya ta gyara mata kanta wanda dama tunda rana tai mata kitso mai kyau kamar sun san da zuwan shi a ranan, Ita kan ta maryam din tasan cewa jikinta yasamu canji sosai, a irin yadda take jin shi, Duk yadda zan yi bayani haduwar ta a lokacin mutun ba zai fahinta ba sai dai inda kungane ta a fili, Sallah Uwale tasa ta gabatar daga magrib har isha,i, ta umurce ta dayi, Amma ita maryam din duk a lokacin ba ta fahinci komai ba don babu abin da ta kawo a ranta, Abu guda ne ya tsaya mata arai shine jin haushin yadda suke ta wani rawan jikin shirya mata jiki kamar wata bakuwan Yusuf din, Bayan yasan ko ya take da tayi ado da batayi ba duk yasa ni, Amma wai yau shine don ance yazama mijin ta shine suke wa ni rawan jiki à kai, Gurin da tai sallah take zaune Uwale takara umurtan ta da takara shafawa jikin ta har zuwa kasan ta Wanan ruwan dan kwalban da ta bata, da farko mai sa ta jin kasala ajikin ta, Bayan ta gama shafawa kamar yadda Uwale ta umurce, tamika mata kwalban, Takoma bakin gado tazauna tare da sake wani irin ajiyan zuciya, Daidai lokacin da Ànty ta tashigo dakin dauke da wani dakakken lace a hannun ta, Mai ruwan sky clour da stones farare ajikin shi suna sa shi shining, Ran ta bai so ba amma ba yadda ta iya dole ta karbi kayan ta sa kamar yadda aka umurce ta dayi, don gudun sabawa manyan ta, Daga bakin kofan sukaji muryan mahaifin su wanda hakan ba karamin haifar masu da kaduwa yayi ba dukkan su, Nan da nan jikin maryam yadauki rawa kamar wace ke jin sanyi, Baba kecewa ina Dijen take ne wai ko ba ta gidan ne, Anty Dije ta karba da cewa ganin baba ya ce to, to , ya kun gama shiri ko, ? Jiki a sanyaye ta amsa mai da fadin eh baba, Ido Maryam ta zaro waje don jin abinda mahaifin su ke cewa yar ta, Fito min da ita kawai maryam ta iyaji a lokacin , Wanda hakan yai daidai da wani irin sakin kuka da tayi a lokaci guda, Na shiga uku Anty inji maryam cikin wani irin murya mai ban tausayi, take fadar haka, Uwale ne da Safiya wace itama dai kukan take sakewa alokacin don ganin irin halin da aminiyar ta yau ta tsinci kan ta, Duk da dai tasan cewa aure bautan ubangiji ne amma sai take ganin mahaifin kawar nata bai mata daidai, ba gaskiya, Anty Dije wace hawayen dake idon ta alokacin suka balle mata itama dai kukan tashiga yi, Jin kukan mu wiwi da baba ya yi, ya sa shi kiran sunan Anty Dije a hassale, Wata, ashar ya wulwulo ya durawa gaba dayan su a tsorace, , Cikin sauri maryam ta koma jikin bango da gado ta kankamay Safiya wace itama kukan takeyi, a lokacin, Baba wanda idon shi suka yi jawur a lokacin sai huci yakeyi, Yakara kiran Anty dije a ciki wani kakausar murya wanda yakara sasu firgita, Wuf maryam din tayi ta cakumi yar nata ta yadda baza ta iya kufcewa ba a lokacin, Shiko baba daga waje sai cewa yake yi yo naga kina son raina min hanakali fa, Anty Dije tace cikin muryan kuka baba ga munan fitowa ai, Kara kankamay Anty Dije maryam tayi tana wani irin kuka cikin sauti mai ruda wakwalwan mai sauraren ta, Cikin kukan take cewa ban san may nayi wa baba yake min haka duk cikin diyan shi anty kodai laifin da mahaifiya ta taimai yake ramawa a kaina, Bakin ta Anty Dije ta rufe da sauri tana cewa maryam kan daya kuwa dakike irin wanan kukan, Safiya tare da Uwale da anty kowa ya hau bakin shi sai magana suke ba maryam din, Kai ta girgiza tace may ye na bani hakuri bayan wanda ma ya kawo ni duniya yana bidan kai dani, Wanan karon bakin nata Anty ta buga da karfi sai da uwale tace mata ta daina dukan ta tabar ta taji da abu guda, Duk zafin rai ne yasa take wanan maganganu bawai cikin hankali takeyin su ba, Mahaifin su wanda yake tsaye daga waje yana jin abin da sukeyi a cikin daki yai murmushi mai daci, Uwale ce tazo gaba da maryam din ta kira sunan ta ahankali tana cewa ki yi hakkuri, Allaj ya kaddarata naki auren zai zo din haka don Allaj kiyi hakkuri da hukuncin da mahaifin ku ya yanke a kan ki, Wani abu ta shafa mata mai sanyi a hanni tace Allah yasa gidan zaman ki ne maryam, Allah yasawa auren ki Albarka yabaki zuri,a dayyaba, Sauran dake dakin suka karba da fadin Ameen ya Allah, Tabbas maryam tasan cewa babu mafita akanta yau tabar gidan yar uwar na ta ke nan, Safiya ce tai saurin goge lalin da a,ka shafawa maryam din a hannun ta, Hannun ta ta diba ashe lalle ne aka shafa mata, shike nan tafaru takare, Wanan karon kukan zuci ne maryam din keyi don sani ba wani makawa a kan ta, sai gidan Yusuf, Ba suyi aune ba saga Baba har cikin dakin nata yashigo ya rike hannun, maryam din wace ke kuka wi, wi, Anty dije komawa tayi falo inda tasa kuka sosai tare da yaran ta , Don dai harga Allah ba haka taso auren yar uwan nata ya kasance ba, A falo daidai inda anty take a saman kujera tana kuka maryam ta daga murya tana cewe, Anty na ki yafe min duk laifin da nai maki don girman Allah, Da wanan maganar tabar gidan yar uwan nata tana rike da hannun mahaifin nasu, Gaba daya yau taji ba Yusuf ba duk wani namijin dake duniya ya fice mata a rai, Suna fita kofan gida motar Ibrahim ce suka gani waje a parke, Wanda dama yana jiran fitowar su ne kawai don haka yana ganin su ya tada motar ,shi, Suna shiga daga ita sai baba kawai don yace bai yarda da rakiyan ko wace mace ba, Maryam wace tadan jin gina kan ta da glass din motar tana kuka cikin sauti mai tsuma zuciya, Muryan babane ke mata nasiha akan zaman aure, da kuma rayuwar duniya har suka isa G,R,A din unguwar da Yusuf ke da gida a ciki,,,, Yusuf wanda dawo wanshi ke nan daga gidan mahaifin jibrin, Wanka yayi duk da yaso ya tafi gidan mahaifin shi kafin ya kwanta don ya kara dubo jikin shi, Amma sai yaji kasalan zuwa saboda hutu kawai yake so don tun da Anty tabashi labari jikin shi yake a mace, Bayan yafito wankane yasa wani jallabiyan shi milk colour mai laushi da sulbi, ya feshe shi tsab da turaren shi yadauko yar tasbahan shi yanufo falon shi, Daidai da zaman shi a falon suma suka tsai,da motar su a kofar gidaYusuf din, Yaron gidan shine ke sanar mai da cewa yana da baki, Sallam Ibrahim yayi inda ya sheda muryan shi sai dai yayi mamakin ganin shi a garin, Zai yiwa, Ibrahim din magana kenan sai yaji sallaman baba a bayan Ibrahim din, Gaban shine ya bada rass don sam baiyi tsanmanin dattijon ba a wanan lokacin, Da sauri ya mike tsaye daga inda yake zaune, bai gama mamaki ba sai maryam da yagani a bayan baba yana rike da hannun ta, tasha lulubi a cikin wani farin gyale mai daukan ido, ga lace din jikin ta na shining a cikin dare, Dukawa yayi cikin rudewa da niyar zai gai da baba, Amma sai baba din yadan taro shi kafin ya kai kasa yana ma cewa, tare da kamo hannun shi, Daga inda maryam din take tsaye baba yadan jaye a tsakanin su yana mai damka hannun maryam din cikin na Yusuf din yace, Karbi ga matarka nan nakawo maka Allah yasa wa auren ku albarka, Sai kai ta hakkuri da halin mata da kuma duniya, Maryam najin irin damkar da Yusuf yaiwa hannun ta sai ta sake wani irin kuka mai shiga rai, da razana rayuwa, Yusuf sai da ya dan rintse idon shin saboda kukan har cikin zuciyar shi yaji ta, Amma sai yadaure yace wa mahaifin su maryam din, Na gode baba Allah ya kara girma da daukaka da izinin Allah zaka sameni mai rike amana, da alkawari, Allah yasa inji baba din ya juya a gagauce yabar gidan yana mai masu sai da safe,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [5/3, 10:53 AM] ‪+234 706 262 3470‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI RAMADDAM MUBARAK👏👏👏👏👏👏👏👏 Baba ya na wuce maryam tasa wani irin kuka mai tsuma zuciya, Wanda kukan ya kara ruda Yusuf a lokaci guda, ya rasa may zai yi,. Rugumota yayi zuwa jikin shi yana dan lalashin ta kamar yadda ake wa karamin yaro, Shhhhh yake fada kamar mai rada ko lalashin karamin yaro, A hankali maryan take dabaran zare jikin ta daga nashi saboda rungumar da yai mata, Amma kuma sai taji bazata iya ba saboda irin rikon da yai mata, Dago kanta yayi daniyar su hada ido amma kuma sai maryam din taki don bazata iya jure hada ido dashi ba, Idon ta a rintse ya dago kan ta, jin ta kara sautin kukan ta yasa shi cewa Am, So, Sorry Sorry pls, Kai maryam ta girgiza mai cikin kuka tace uncle ka daina bani hakkuri pls, mahaifina da yar uwata da,nafi so aduniya, yau sun nuna min rashin kauna, karara, Sai kuma ta sa wani irin matsanacin kuka alokacin Yusuf ya rasa may zai mata a lokacin don duk kukan nata yasa shi cikin wani rudewa, A, hankali ya kara jawo ta zuwa jikin shi, yace cikin murya mai kama da rada, Baba na son ki maryam haka ma Anty kawai dai a haka al,amarin namu yazo, Don Allah ki kwantar da hankalinki ki daina kuka pls, don muyi magana ta fahinta pls, Jin ta dan sassauta kukan nata ne ya sa shi riko mata hannun ta, Hannun nata ya ja zuwa kan kujeran da ke kusa da su, Zaunar da ita ya yi yana fadin ya isa haka, Maryam, Cike da tausayawa yake maganar yana kallon ta cikin damuwa, Azaton maryam saman ciyan ta tasa kan ta sai dai bata san cewa a jikin Yusuf din take ba, Can kuma jin duk sunyi shiru sai kayan na,urorin dake aiki a falon yasa maryam din daga kanta kamar tana diban wani abu, Kan shi yadan sunkuyo daidai saitin kunnen ta yace may kike son yi,, Alwala tabashi ansa a takaice, Kusan a tare suka mike daga zaunen, Amma sai yace mata yana zuwa dole taja tai tsaye guri guda ga juwa na diban ta, Security din shi ya sallama da sutafi hotel din yai masu masauki har zuwa gobe, Don dama ba anan suke kwana da shi ba, hotel ne yake kama masu, Agogon bangon dake falon ya kalla a lokacin karfe, tara da rabi na dare, Da hannu ya nuna mata hanyar shiga inner room din nashi yakuma nuna mata, hanyar bathroom, Ganin jirin na kwasan ta tana dan dingisawa, yasa shi saurin kama mata hannun ta, Ya taimaka mata har zuwa cikin bathroom, din suna kai bakin kofa sai ta tirje mai don haka ya gane nufin ta sai yaja baya Murmushi yayi yaja bayan yana cewa kiyi a hankali kada sulbin ties ya kwashe ki, komawa yayi daga baya inda yafita daga cikin dakin, A hankali ya sauke numfashin shi saboda irin yadda ya ji lokacin da maryam din take a jikin shi, Idon shi ya lumshe yayi da ya harde kafan shu guda cikin guda, Yadan jin,gina bayan shi ga bangon falon, Yasan cewa yasha rungumar mata har yana iya kwantawa da mace a gado guda , Sai dai bai taba jin wani abu akan mace ba irin yadda yaji yau din, Bude rinanun idon shi da suka kada sukai ja alokaci guda yayi, Ya furzar da wani irin iska mai dumi daga bakin shi, Sai kuma ya kara rufe idon nashi wani irin bakon yanayi yake jin yau ya ziyarci zuciyar shi, Jin motsin ta da yayi alamar ta fito daga bayin yasa shi saurin dagowa daga gurun da yake tsaye rufe kofan gidan nashi yayi Sanan ya koma gurin ta a dakin a lokacin tana kokarin gyara daurin dankwalin ta, Nan idon shi yai araba da kitson da Safiya ta yarba mata dazun da rana, Carpet din sallah ya shimfida mata da kan shi , Shima alwalan ya shiga ya dauro duk da yasan cewa yana da alwala a jikin shi to amma dole ne yasake saboda yanayin da ya shiga, Ya kai tsawon wani lokaci zaune ya jero addu,oi daga bakin shi, Addu,oin da suka ba wa maryam mamaki don bata taba tsan manin cewa yasan dasu ba, Duk da kanta a duke yake a lokacin hakan bai hanata cewa amin ba , Batayi aune ba sai jin hannun shi da tayi a saman kan tadake duke a cikin jikin ta, Muran nan tashi irin ta mai rada ko kuma wanda akasa yin magana dole yace, Maryam ina fatan zaki rike rikon amana arayuwar zaman,mu, Zaman ya zamace ta dindin wace ba rabuwa a tsakani saidai lokacin da Allah yai na shi iko akai, Dafatan zaki cire duk wani damuwa da shaku a kaina ki rugumay da hannu bibiyu a matsayin mijiki, aminin ki kuma dan uwan ki, masoyin ki, Wani sautin kuka ne yakara subbacewa maryam din a lokacin, Ido ya kura mata kawai daga gurin da yake yana dan jan tasbahan dake a hannu shi a hankali, Kyaleta yayi tai kukan don yana ganin idan bai bari tayi mai isar ta ba zai iya haifar mata da fever a kar she, Mikewa yayi daga gurin ya kashe fanka din dake aiki yakunna masu A,C dakin, dake can mane saman , Duk da dakin nawani irin bala,in kamshi amma sai da ya kara fesa room fresh, Duk cikin yanayin kuka da take, kukan nata,bai hana ta shako, kamshi da sanyin da suka gauraye dakin a lokaci guda ba, Falo ya koma sai gashi dauke da kwalin madara a hannun shi tare da wani leda, Mamaki kwarai na yadda Yusuf yasan irin wanan sunar mai karfi a cikin addini, Sunnan da bakowa ango ne yasan darajan ta ba har yake daukar ta da karfi ba kamar yadda mazon rahama ya umurta, ayi, Muryan shi taji gab da kunnuwan ta yana mata tayin madaran Ta so ta share amma sai nasihan baba ya fado mata a rai inda yake cewa Yi nayi bari na bari shine albarkan aure ga duk wata diya mace wace ta san kan da kuma addinin ta, Don babu wani abu gadita mace da ya wuce biyayyan mijin ta don shine tafarkin shigar ta aljanna, Taso ta karbi cup din daga hannun shi amma sai taga baida niyar bata, Don haka ta daure ta dan yi kurbi sau biyu sai tadan kau da kai tace na gode, Murmushi kawai yayi alokacin tana kokarin kara dan kwantar da kan ta cikin jikin ta, Da hannun shi ya yago cinyar kazan yana kokarin kai mata a baki, amma sai tacd cikin wani irin murya nagode bazan ci ba, Bai matsa mata ba don yasan cewa abinda take ji shima yana jin shi don ko wanan kazan a hanyar shi tadawowa daga gidan mahaifin Jibrin,yadan tsaya kaza, abincin kowa ya saya, Badon yana jin yuwa ba saidai don dare kawai saboda tun lokacin da Anty Dije tafada mai zancen auren su da maryam, Yake jin shi wani iri har yuwan da yake ji kafin ya shigo gari duk yadaina jin shi, Toilet ya dan leka yawanko hannun shi tare da kara dauro alwala, Al, Kur,ani mai girma dake ajiye a gefen shi ya bude yadan fara karantawa, Saboda samun natsuwa don jin shi yakeyi wani iri a lokacin , ARRAHAMAN yake karantawa abinda yai matukar bawa maryam mamaki saboda irin yadda Yusuf yai saurin sani addini haka, Daga inda take zaune take sauranren shi cikin mamaki da burgewa, Wani irin natsuwa ne da tawakkali ya ziyarci zuciyanta a lokaci guda, Tun tana sauraren shi, har barci yadan yi kaman yafara daukan ta Can kuma komay ta tuna sai ta sa wani irin dan she,shekan kuka a lokacin, Azatonta kukan bai fito fili ba saboda ta dauka aciki, ciki takeyin shi, Bata aune ba sai jin hannun Yusuf tayi a kafadan ta yana mata magana acikin rada ki tashi ki kwanta maryam kada ki sa wanan kukan a,gaba, haka na pls, Tankar bada ita yake magana ba hannunta ya danke a cikin nashi yace, My,goodness maryam bazaki daina ba ki kwanta haka na pls, Cikin sautin kuka tace kabarni a nan ma is ok zan iya yin barci ai,, Sautin murmushinsa ta jiyo, san,nan ya dan matso, dai,daikunnen ta ya ce, Kinsan ai babu yadda zan barki a nan da ke da gidan ki, Amma zan iya kyale ki yanzu inbi umurnin ki in barki ki samu natsuwa, Amma pls ki daina wanan kukan haka don matukar zanga hawaye wanan kyakkyawan fuskan bazan iya samun natsuwa ba,, Fuskan ta ta kawar gefe guda azuciyar ta tana tunanen irin halin Yusuf, Yakai wani lokaci yana karatu itako tana sauraren shi, Ko da ya idar ya waiga gurin da take sai yaga barci ya dauke ta ko, Mikewa yayi batare da ya tashe ta ba har ya gama duk wani abu da yake da bukatan yi kafin ya kwanta, hadari ne ya,taso dauke da iska maikarfi, Fuskan shi dauke da Murmushi ya sake alokacin da ya ganta adunkule guri guda, Yace trouble wife, gurin da take kwance yanufa ya tashe ta a hankali, A hankali yake ce mata hadari ne mai dauke da iska Hakan da taji yasa ta saurin dan mikewa don bata kaunar hadari mai iska, sam, Gefen gadon da ke dakin yai mata jagora zuwa, A hankali ta zauna abakin gadon kanta still lulube da gyalen ta dake a jikin ta wanda ke ta kamshin turaren da Safiya ta safe shi da shi Sai a lokacin maryam ta dago kai tadan kalli gurin da Yusuf din yake tsaye, jikin bango yadan harde hannayen shi guri guda, A sanyaye ya dan girgiza mata kai alamar kada tayi wani kukan, Inda ya karaso gurin da take, zaune shima zaman yayi a hankali gefen ta,, Filo ya nuna mata alaman ta sa kai, tare da gyara mata, kamar wata jaririya , Daga haka ya mike yafita dakin, falo ya koma yadan zauna da niyar ya kwanta a gurin, Amma zaman shi bada wani dadewa ba ruwa mai karfi ya gwauce a garin, Jin yadda isaka da ruwa mai karfi yakeyi da rufin ginan su, yasa shi komawa cikin daki, Kwance yasa may ta saye da kayan dake jikin ta ga gyake duk ya nade ta, Matsawa kusa yayi da niyar yadan zare mata gyalen don kada ya shake mata wuya, Barcin ta takeyi hankali kwance sai,dai a takure take guri guda kamar mai jin sanyi,, A hankali yakai hannun shi ya dan kama jan shi gyalen na ta sannu, sannu ta yadda bazata iya tashi ba, Bayan yacire ya sai yake karewa maryam din kallo komai na ta sha,awa yake bashi, Duk wani halittan ta anmatashi daidai dan das dashi, Rigan dake jikin ta na lace don haka yai niyar cire mata, Amma kuma ya kula cewa akwai zip a bayan rigar, A hankali yakai hannun shi yadan zuge zip din a take idon shi yai arba da halittan gaban ta, Ga wani kamshi dake fisgan shi tun shigowar maryam din gidan inda bai ko son yai minti daya bai shaki kamshin ba, nan mai tunzurashi ba, A take duk wani tunane na Yusuf din ya sauya a lokaci guda , A cikin barci maryam din ke jin abinda ke faruwa da ita sama,sama, Tun tana zaton a mafarki ne har ta bude idon ta tamgararan, Idon ta ta runtse tare da fitar da wasu hawaye masu zafi da radadi, Cikin wani irin murya take mai magana Da kyat ta iya furta kalman Uncle, Dan girman Allah kayi hakkuri kada ka kai min haka pls, Amma ina tankar kara tunzura shi ma maganar ta yake yi don ji yake tankar wani radane ko sallon so take gwada ma shi, Yusuf wanda bazai iya cewa ga duniyar da yake don karon shi na farko kenan ya kasance da mace sosai irin haka, Duk yadda Maryam taso ta hana Yusuf din hakan bai yi ba, Don wata irin mahaukaciyar soyayya ya nuna mata wanda shi kan shi bai san zai iya yiwa mace hakan ba, Har zuwa lokacin da gurin shi ya cika akanta, ya kai gare ta ,,,,, Asuban farko Yusuf ya,farka cikin kasala da rashi karfin jiki, Sai a lokacin yatuna da cewa maryam tana gidan wace kusan kwana tayi tana sheshekan kuka, Saida sanyin asuba ya zo itama ya kashe ta, alokacin shima yadan runtsa, Da kyar yadan lallaba ya sauko da kafan shi kasan gadon, Bathroom ya nufa don yadan tsarkake jikin shi da sauri don ya samu yagabatar da sallah duk da yau jam,i ya wuce shi,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA,,, 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI RAMADAN MUBARAK,👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Kwance take kamar yadda yabar ta kwancen cikin blanket,, Don haka ya tada sallah batare da ya tashe ba, A can cikin barci ne take jin sautin karatun shi sama, sama Da kyar ta iya bude, idon ta a hankali ,ahankali, har kallon ta yai kai gare shi, Bin yadda yake sallah takeyi da ido, sai abin yabata mamaki, Sai alokacin ne ta abinda yafaru a daren jiya ya fado mata a rai, Cikin wani irin jin zafi ta runtse idon ta, a hankali tare wani irin hade bacin rai, Sai alokacin ne taji ajikin ta cewa bata da komai daga cikkn ta, Cikin sauri takara jan bargon dake rufe ajikin ta tana mai kara shigewa ciki, A lokacin ya idar da sallah ya dan shafa addu,a sama, sama, Muryan shi taji yana cewa ki daure ki tashi ki dan gyara jikin ki yi sallah don lokaci ya ga ba to, Ganin bata da niyar tashi Yusuf din yashafa addu,an dayakeyi a jikin shi, cikin tsanaki, Mikewa yayi tsam zuwa bakin gadon ganin ya nufo ta yasa maryam ta runtse idon ta gaba cikin jin kunyan shi da nauyi, Muryan shi taji gab da kunnuwan ta cikin rada yana cewa sorry barin tausaya maki, Hannu ya mika da niyar kamota cikin wani irin ka murya mai ban tausayi take cewa, Nooo, pls uncle, katafi kawai, kaje kaje pls kaje waje zan tafi, Tsayawa yayi yana kallon ta cikin wani irin tausayawa, Tambayar ta yayi da cewa zaki iya mikewa ke nan ko ? Ganin da tayi cewa idan bata ansa mai, ba bazai barta ba ya sa ta ansa mai da kai ta cikin bargo tana cewa, tafi zan iya, Fita Yusuf din yayi cikin jin tausayin ta saboda yasan cewa bai kyauta mata ba, Saboda bai raga mata ba sam duk da yasan cewa shima ba laifin shi bane bai so hakan ba, Kawai tsintar kanshi yayi da ganin shi dumo, duma tare da ita, A hankali ta mike zaune tadan lalaba ta sauko da kafanta, kasa, Da bin bango har ta isa bathroom din inda tasamu ya hada mata ruwa masu zafi, Sosai maryam taji dadin wanan ruwan inda tadan dauki lokaci a cikin shi har sai da taji cewa tadan samu sa,ida, Falo yake zaune amma tunane yakeyi ko wasu kaya maryam din zata yi sallah da shi, idan ta fito, Sai da ya kwatanci cewa ta shiga bayin ya koma cikin dakin, Wani jallabiyan shi baki yadauko mata inda ya aje mata a bakin gado tare da aje mata gyalenta a saman gadon Sauran kayan gaba daya ya hada su guri guda yakai, gurin laundry, Bayan fitowar tane taga wanan jallqbiyan tare da gyalen ta don haka tagane nufin shi, Ba bata lokaci ta dauka tasa tare da daure gyalen a wuyan ta, Tsab ta gabatar da sallah ta tare da daga hannayen ta sama tana kwararo addu,oi Sai hawaye ke zubowa daga idon ta kamar anzubo ruwan sama, A hankali ya iso gurin ta inda yadan dago ta fadawa tayi saman fadardar kirjin shi Wani irin kuka takara sakewa cikin wani irin shagwaba, wanda ita kan ta batasan, ta na yi ba,, Mai,da ita yayi saman gyararen gadon da ya gyara da hannun shi yau, batare da yajira mai gyara ba, Kwantar da ita yayi a hankali saman gadon ba musu ta kara kwantawa saboda tana bukatan hutu a jikin ta don yasan bai sarara mata ba,sam Don haka tausayi ta bashi saboda ko inba aure ba ya za,ayi wanan yariyar har ta dauke shi haka, Ba bata wani lokaci takara komawa barci cikin gajiya da kasala,, Falo ya koma cikin wani irin yanayi da yake jin kan shi yau wanda bazai iya mussalantawa ba, Zaune yake yana tunanen shi may zai iya yi wanda zai sakawa wa yan nan mutane da wanan irin alherin da sukai mai, Mahaifin jibrin gashi sam ya ki karban kudin da sukai mai sadaki da sauran dawainiya, Ashe akwai mutane masu irin wanan a,kidar a duniya, A gaskiya wanan halin saidai musulmai hausawa don dai yan kabilar su bazasu taba iya yin wanan halarcin ba, Gaskiya shi bai ma san ya zai iya kwatanta halarcin wa yan nan mutanen, Gashi yau dattijo yai mai wanan irin alherin da ba zai iya kwatantawa ba, Saboda a duniya bai taba sanin cewa haka mace take ba, sai daren jiya, Jiyan kwana yayi yana,sawa mahaifin maryam addu,a a cikin zuciyar shi, Kofan gidan nasu yaji ana kwankwasawa, cikin mamakin kowaye ke mai sallama awanan safiyan, Mikewa yayi zuwa kofan falon inda yake jin ana buga kofan, Safiya ce tsaye hannun ta dauke da basket mai dauke da kuloli da kuma flask na ruwa, Duk ta dan jike saboda dan yayafin da ake yi a garin, Hanya shigowa falon yadan bata tare da kauce mata, Sai alokacin yaga dan trolley din dake bayan ta na kayan maryam, Taimaka mata yayi ta shigo da kayan inner room ya shiga da kayan inda ita safiya din ta wuce da basket din gurin dining, A kwance ya samay ta ta dunkule guri guda alamar, tana cikin dan yanayi, Batare da yatashe taba yabar dakin yakoma falo gurin safiya, Zaine ya samay ta a saman kujera tana dan raraba ido ko zataga fitowan safiya, Sai da ya zauna saman kujera da dan murmushin shi sanan yake ce mata maryam din na daga ciki tana barci,, Yace don Allah ta taimakawa maryam din don tadan samu ta sake jikin ta, Jiki ba kwari safiya ta mike zuwa cikin kuryan dakin, Maryam dince tagani a kwance saman gado cikin wani irin yanayi na ban tausayi, Tausayin aminiyar na,tane ya kamata, don tana ganin ta tagane cewa a kwai abinda ya wakana a tsakanin ta da Yusuf din, Cikin barci maryam din taji nauyi kamar da mutum a kusa da ita a lokacin, A hankali ta bude idon ta, ya sauke su ga safiya din wace ke zaune gefe tana karawa dakin kallo a cikin tsanaki, A hankali maryam din ta furta sunan Safiya din wanda yasa safiyan juyowa da,sauri, Maryam din ta yun,kura da niyar mikewa zaune amma sai taji wani irin ciwo daga kasan ta, Hakan yasa ta komawa da sauri ta kara kwantawa, Safiya tadan mike tsaye ta je gurin kanta ta dan gyara mata filon ta yadda zata ji dadin mikewa daga kwance Da taimakon ta tasamu takai zaune amma kuma sai kuka ya kubce mata, Safiya da kyat ta hade nata kukan tawayan ce da cewa haba maryam wanan kukan tun jiya kina ta abu guda ai yakamata ki ba kan ki lafiya hakana pls, Hakana ta nuna wa aminiyar nata cewa bata fahinci komai ba akai, Ki tashi ki shirya muje falo ki karya pls, ba musu maryam din ta daure cikin cijewa ta nufi bathroom inda tadan kara gasa jikin ta , Hakan yadan sata kara jin dan karfi a jikinta wanda yadan saita mata tafiyan ta, A saman gado tasamu safiya ta fitar mata da wasu zani da riga na atamfa Atamfar kore mai dan adon flowers ruwan kwai da fari, fari, Dinkin fitted ya amshi jikin ta cikin kayan da yay iliya mijin anty ya dinka matane da sallah, Ta gama sawa tana kokarin daura dan kwali a kanta ne, Yusuf din ya shigo dakin kallon ta yayi yaga takoma mai wata sharrr da ita, Har gurin da take tsaye bakin wani dan mirror ya karaso Ta bayan ta ya tsaya suka hada ido daga cikin madubin , Cikin sauri maryam din ta dukar da kan ta a kasa saboda kunya da nauyin shi da take ji, Murmushi yayi ya karaso gaban ta ya sa hannayen shi ya rungumota zuwa jikin shi ta bayam tare da shakan kamshin jikinta, Sai da yawani ja numfashin shi ta yadda har tana iya jin shi sanan ya ce a hankali I love you maryam with all my heart, Thank you, for being, with me, yesterday night, Idon ta ta rinstse tare da tarso wa wasu hawaye masu dumi acikin zuciyar rayuwan ta na ce mata yau ita maryam ce ta kwana da namiji, Kara matse tayayi zuwa cikin jikin shi gam kamar wanda za a kwacewa ita, alokacin, Zuwa wasu yan second's sake ta a hankali tare da wani jan numfashi, da ya sauke a hankali, Cikin muryan tashi yai mata magana kamar da a kunnen ta yace Safiya na falo tana jiran ki da abinci, Zarare jikin ta tayi a hankali daniyar wuce wa amma sai taji ya rike mata hannayen ta Dago kai tayi tafan kalleshi cikin dan yanayin pls Murmushi yasakar matata tare da sake mata hannun har tafara tafiya taji muryan shi yana cewa pls, You should keep our secret , Kafin ya karasa tadago manya manya idanuwar ta taimai wanin kallo mai kama da harara, Yana mai kallon ta har fice daga daki inda tafiyan ta yai bala,in bashi tausayi, sosai, Safiyace ta samu a falon tana zuba mata pepper soup din kayan cikin rago a cikin wani plate mai dan zurfi, A lokacin da maryam din ta dan ja kujera guda tadan zauna, Ganin plate guda da cibi guda yasa maryam din dago kai takalli aminiyar nata tace, May kike nufi da samin cibi guda aciki, muryan tama alokacin jin shi abin tausayi ne, Safiya tace kedai ki karya don nasan haka kika kwana da yuwa jiya, Idon ta ta lumshe saboda ambato jiya din da safiya tai mata, Daren jiya karshen bakin cikin mai kunci, daren jiya ansha da wandake yin barci kar ku taba kaifin ta yafi na aska, Safiya ta ce kisha mana maryam ga tea nan mai zafi a gaban ki, Cikin daure fuska maryam din tace, idan bazaki sha ba malama ki fada min in tashi don saboda ke nake zaune a nan, Safiya wace bata da wani zabi akai dole ta jawo kujera guda ta zauna tare suka shakomai da maryam din, Sun kusa gamawa ne Yusuf din yafito cikin wasu Indian yard masu laushi da sulbi, Sai kanshi ke tashi kamar wa a company turare, Plate din yakai idon shi akai inda yaga ba wani abin kirki suka shaba, Safiya ce tace mai uncle ga abinci a zubane yanzu saida yadan kalli maryam din sanan yace , I hope madam ta ci ita ko ? M Safiya tadan yamutsa fuska tace ba sosai ba dai Maryam tadago idon ta takalli safiya din kamar wace zatai magana sai kuma tai shiru, A hankali maryam tamike zuwa saman daya daga cikin kujerun dake a falon, Inda itama,safiya ta kwashi kayan da,suka bata zuwa kitchen din gidan, Yusuf ne ke cewa ta ahe da akwai wanda zai zo ya wanke su, anjima, Amma sai safiya din tace bari kawai a wanke kada su bushe a hakan, Zama yayi yadan zuba kadan ya fara sha amma sai yaji cewa bazai iya ba shima saboda cikin shi da ya kulle mai, Amma yadan daure ya sha da dan yawa kadan gudun kar wani ciwo ya kama shi, Mikewa yayi yana cewa a daidai lokacin da safiya din tadawo daga gurin wanke kayan, Zan je ingaida su baba da gidan mahaifina, Daga haka yadan kara gab da inda maryam din take kwance batare da jin nauyi ko shakkun safiya ba yakaiwa maryan din dan pick kiss a goshin ta, Safiya tazo kusa da inda maryam take zaune nan tafara bata labarin bayan tagiyan ta jiya, Da irin yadda Anty tai kuka sosai bayan tafiyan ta, Dakuma shigowan da baba yayi gida,yau da safe Inda yake ta sa masu albarka tare da fatan samun zuria masu albarka, Maryam wace tadan kai kishin gide tadan lumshe idon ta saboda irin yadda take ji azuciyar ta, Daga haka safiya tana mata hira barci mai nauyi ya kara kwashe ta, Hakan yabawa safiya din dama tashi tagyara masu gidan tsab, Yusuf ne zaune a gaban baba shida Jibrin da KB da Ismail, Inda baba ke kara yiwa Yusuf din nasiha akan zama da iyali wanda hakan gaba dayan su sun ji dadin karin hasken da dattijon yai masu akan hakkin zama da iyali, Wanda akasarin mazan yanzu suke subar da daman su saboda son zuciya, Dagidan baba suka wuce gidan mahaifin jibrin din inda shima yai masu irin nashi gwargwadon fadan kamar yadda ya kamata, Dafa can suka nufi gidan Abdulsamad shima yai ma Yusuf nasiha so sai akan sai yakai zuciyar shi nisa saboda yan uwan shi, Da kuma matar shi don zasu dinga kawo mai fitina iri, iri, Musalai kala kala dai yaba shi Yusuf din wanda sai da ya kara jin jikin shi ya mutu, Sai bayan wani lokacine yakoma gida alokacin maryam tana falo kwance tana barci cikin gajiya, Ginin tare da abokai yake yadan sa shi shafa mata fuska ahankali wanda hakan yasa ta bude ido sukayi arba, da junan su,,,,,,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 8⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Ya Allah kaja kwanakin mu izuwa watan RAMADAN, kuma Ka Azurta mu da A dake cikin watan. Ameen Ya Allah, RAMADAN MUBARAK👏👏👏👏 ANTY NA, NAFEESAT HARZAMI TAREDA ANTY SAFEENAT wanan shafin nakune ku kadai fatan alheri gare ku akoda yaushe, Sallama,sukaji daga kofan gidan azarin Yusuf su Jibrin ne amma kuma sai yaga ai matane, Safiyace tai masu iso, da su karaso zuwa cikin gidan, Dauke kowancen su take da robobin cincin da aka soya, Har guda shidda ko wani roba da nau,in kalar abin da ke a cikin shi, Tundaga dubbla guguru tsatsafa alkaki, dakuwa, da sai Donot, , Biyun wa yanda ba su kai shiddan girma ba naman kaji ne aciki soyayyaye, Ba Yusuf ba har maryam din tana kallon wa yan nan kayan da mamaki, Jibrin ne da KB suka karaso ciki tare da,sauran mata, Matar mahaifin maryam kishiyar maman Anty Dije itace ke ce,wa Yusuf babane yace a kawo mai, shi da mahaifiyar maryam, Yayi hakkuri da su saboda bai samu hadowa da kayan abinci ba abin yazo a girshi, Kallon robobin yakeyi batare da yasan abinda ke a ciki ba, Safiya ce tare da uwale, suka dinga bude robobin wani irin nauyi da kunya ne suka kama Yusuf a lokaci guda, Maryam uwar kuka tana gefe idon ta ya wani ciciko da hawaye a lokacin, Saboda tunanen da takeyi na cewa ina baba suka samu gidin yin wanan abin haka, Tashi tayi tsam ta fada daki Yusuf wanda alokacin badon idon mutane ba ji yayi kamar ya rungumota, Wanan matar mai magana na farko ke cewa sai zancen kayan gadon ta da sauran kaya zuwa gobe za,a kawo matasu gaba dayan su, Cikin rashin fahintar zancen su Yusuf yafita inda su ma su KB da Jibrin suka bi bayan shi, Fitar su yai daidai da mikewan uwale wace tabi bayan maryam din, Zaune tasamu maryam abakin tamgamaymay gadon dakin, Saida takarewa dakin kallo cikin kada kai ta zo gurin da maryam take zaune, Jin shigowar ta yasa marya dan dago kanta idon ta taf da hawaye take kallon uwalen, Tambayan da uwale tai mata yaba ta mamaki sosai, Don ce mata tayi injin kin ta shiga ruwan zafi don tafiyan ki ya koma daidai, Lokacin ne safiya ta shigo dakin ta wuce bathroom din nan ta kara hadawa maryam din ruwa masu dumi Zaune suke suna hira har tafito daga bayin tare da dauro alwala, Jikin ta yadan koma mata normal gefen safiya ta zauna, a,nan uwale ta shiga yiwa maryam din bayanan kissan zama da miji da yan uwan shi, Tai mata bayani akan irin kayan matan da ya kamata ace maryam din tayi amfani da,su wanda zai kara mata haske a zuciyar mijin ta, Uwale tace maryam nasan cewa ko a haka na barki bazaki taba wulakanta aidon mijin ki ba saboda Alhamdullahi kin samu duk wani horon da ya dace ki samu ga namiji, Iyaka dai yadda zakiyi amfani da shine yanzu sai kin yi da gaske, Yusuf yana fita waje tare da abokan shi yaja ya tsaya a bayan motar shi hannayen shi harde da juna, Cikin marairaicewan murya yace wanan abinis too much for me, Pls Jibrin ka gayawa baba cewa yadakatar da mahaifin su maryan hakana, Matar da yaban kawai ya wadatar dani ga komai na duniyan nan, Banda abinda zan saka mai dashi sai dai godiya saboda ya mai dani cikkaken mutum Ya, bani macen da ban taba sanin cewa zan ita mallakan irin taba aruyawa na, Da sauri su KB da Jibrin din suke kallon shi don jin abinda ya ce daga karshe, Yadaga gira tare da kallon ido da ido yace mace kamila mai tarbiya ga mutunci da girmamana gaba wace ta rike darajan ta da martaban ta har zuwa ga mijin ta awanan zamanin ai tafi ko wace mace zama mafi daraja da kima, Sun gane mai yake nufi da hakan gaba dayan su suka ansa da fadin hakane, Don gaskiya Yusuf ya fadi irin wa yan nan matan matane na rufin asiri, Don akasarin su da wuya ka samay su da wani matsala a rayuwan aure, Dafa Jibrin din yayi yace mai ya kamata mu gagauta zuwa don baba ya samu wanan tsohon yai mai bayani yadai wani shirin kawo wa maryam kayan daki, Mr Emanuel yana tsaye bakin kofar gidan shi rike yake da wani karfe da akatokara a tsakiyan gidan, Motan Yusuf ce da ta shigo gidan yabi da kallo har zuwa inda ya parker ta, Shima Yusuf yaji dadin ganin mahaifin nashi a tsaye alaman yaji sauki ke nan, But ya bude masu aikin gidan ne sukazo da sauri suka fara fito da robobin da Yusuf ya,zo da shi, Cikin gida suka shiga dashi shidai tsohon yana tsaye a kofa yana kallon su, Bayan shigan su ciki sun zauna sai ga Samuel da Esther kaunar Yusuf sunfito, Acikin yare suke magana tambayan shi sukayi da yare may ya kawo masu haka, Esther ce ta bude robobin gani abin da ke cikki yasa ta fito da ido waje, Mr Ema ke tambayan dan nashi kayan may wanan haka , Ba wani tsoro ko jin dari Yusuf yace wa mahaifin nashi wanda duk ya tsure shi da ido cewa Kayan aure nane nakawo maku don kusa muna albarka akai, Kafin ya karasa zancen shi yaji muryan mahaifin nashi cikin mashifa yace, God forbids bad things, Joseph are you out of ur mind,? Sai da sauran yaran suka dan kadu saboda action din mahaifin nasu, irin yadda yayi, Yusuf wanda dama yasan cewa za,a rina don haka ko gezau bai yi ba sai kallon mahaifin nashi yakeyi da addu,an shi abakin shi, Maimakon fadan da Ema din yai niyar yiwa yaron nashi sai kawai daga mai hannu yana cewa park your things and go pls, I don't want to see it here, Esther wace ke tsaye daga kofa cikin wasu yan kananin kaya tace no, no papa , We want to test it , Is our brother weeding pop,,, Kallon mamaki mahaifin nasu ke wa Esther din wace har takai ta fara daukan guguru guda tana kokarin kaiwa ga bakin ta, Cikin wani irin daka tsawa uban yai wa Esther, magana har sai,da ta dan kadu, Cikin dan turo baki tace me, i wan eater woo, Tadauka takai ga bakin ta inda shima Yusuf, din yadan gutsura ya kai abakin shi , Samuel wanda ke gefe shima ya jawo nashi rabon a gaban uban suke ta cin abinsu suna hira hankali kwance, Yusuf ya umurci kaunar shi da ta sam ma yan aikin su don suma su sheda, Mr EMA wanda ke zaune murtun da fuska ya rike sandan shi ta sarautan su na IBO Yace wa Yusuf yasan da cewa zai auri yar kabilad IBO nan bada dadewa ba, Murmushi Yusuf yayi yace indai, musulmace may zai hana ya aure ta, Amma idan ba musulma bace ba zai yi ba, Duk mamaki maganar shi tabasu taya zai ce zai kara aure bayan yayi aure soon, Amma rashin sani yasa su daukan cewa kila don dan uwan nasu yana musulmi ne, Yadan dauki lokaci kadan ya bar gidan inda ya wuce ya kaiwa Abdulsamada nashi tare da Naimat, Wace ke fama da laruran ciki a lokacin kamar za ta mutu, Daga gidan ya wuce gidan Anty dije wace,kusan tun jiya baije ba, Inko ba wanan dalilin ba ya za,a yi har ya kwana bai zo gidan na Anty shi ba, A kofan shiga gidan yadan tsaya sai da yai gyara murya,tun daga nesa Sanan ya kwada sallama kamar wani bako, Jin muryan shi yana sallama a kofan gida yau, Mamaki ya kama anty dije wace ke zaune tare da uwale suna ,zance akan auren, Da sauri anty tamike cikin mamaki ta leka har kofan inda yake tsaye, Bakin shi yana rawa yace, Anty ina wuni, ya gida da yara,? Ikon Allah inji Anty Dije din, Cikin mamaki tace Yusuf yau kuma a,waje zamu gaisa haka dakai,? Murmushi yayi yadan sosa kai, nadauka ko akwai mutane ne acikin gidan, Cikin girmamawa ya dan rusunna kasa ya ce,Ina wuni Anty ? Ya gajiyan jama,a ? Wanan karon bata tsaya ba juyawa tayi zuwa cikin gida tace, Alhamdullahi shigo don Allah ba kowa uwale ce sai yaran ka, Wanan ranan abinda Yusuf yai mata yabata mamaki don koma mata yayi tankar wani bako, a gidan, Sun kusa kai wani lokaci a zaune Anty Dije da uwale suna kara bashi magana, Ya mike cikin jin nauyi yana masu sallama,da niyar wucewa, Ita ma Anty mikewa tayi a lokacin tana cewa Yusuf may yasa ka hana baba ya kaiwa maryam din kayan daki, Bakin shi yana rawan bada ansa yace, Anty aiko bani maryam ta aura ba, zan iya yi mata komai daya dace, Don Allah baba yayi hakkuri pls, ba wai na raina bane, Duk ka duka kwana nawa zamuyi a garin kinga ke nan kayan ya zama, barnan kudi, Anty tai murmushi ta gyada kai alaman hakane, Har zai fita sai kuma yadan ja ya tsaya yace Anty don Allah ki ba wa baba hakkuri, Akan zancen lefen maryam din sai na,koma Abuja sanan zan sa a hada mata komai kamar yadda ya dace,, Yusuf , inji anty maryam tace wanan zance ai yanzu ba namu bane Mafanar kace kai da matar ka don ita keda abin ta, Yadda duk kukayi a tsakanin ku ya wadatar da mu don haka mu nan babu ruwan mu, Godiya yai mata yai mata sallama akan ,ai tafi , Hanyar shi takomawa gidane ya tsaya ya siyo masu fruit's kala kala Gidan yai shiru kamar babu kowa aciki baka jin komai a lokacin sai karan na,urorin dake falon, Sallama yayi tun daga bakin kofan yadan tsaya kamar wanda ke jiran iso Daga kofan falon ya cire takalman shi inda ya dan tsaya daga shi sai sock's a kafan, Sai faman baza ido ya ke yi ko zai ga maryam a falon, Sai dai Maryam din bata falon a lokacin, Son ganin maryam din ya keyi a lokacin faren manyan idon ta yake son yin arba da su,, Safiya ce tafi daga cikin kitchen din dauke da wani dan roba, a hannun ta, Sannun da zuwa tai mai gami da karban ledan da ya shigo dashi gidan ga hannun shi, Saida ta aje ledan sanan ta danyi wa maryam din flashing ga,waya, Maryam din tafito saye cikin wani dogon riga na shadda, dark pink, Tasa wani mayafi mai fari, shara shara a saman rigar na ta, Fuskan ta yasha gyara kamar wace zata gurin buki a lokacin, Takalmin kafan ta hill shoes fari ne mai fari sol so sai din nan Tasa wani abin hannu fari mai farin sarka a wuyan ta, Maryam tayi kyau sosai da wanan kwalliyan , a hankali take takowa daga corido din zuwa inda yake, Har ta iso gaban Yusuf bai iya magana ba sai ajiyan zuciya da yake ta faman saki,a hankali, Gefen kujerar da yake zaune maryam din tadan zauna gami da yi masa sannu da zuwa, Shakan kamshin maryam din yayi nan take yaji wani irin natsuwa da bai taba ji ba ya zo mai, Safiya wace ke gidan a lokacin itace ta tajawa Yusuf burki a kan irin yadda yake jin maryam din, a lokacin, Safiya ce tafito daga cikkn uwar dakin sagale da jakar ta tasa hijab din ta, Maryam cikin muryan nan nata mai kama da ta rowa tace wa safiya din, Ke kuma ina zaki kuma, ? Safiya wace ke ta kokarin gyara hijabin ta tace au so kike dama in kwana nan, Ina na gyara maki ko ina yadda ya kamata to may kuma,zan tsaya jira, again, Haba Yusuf wanda wani irin farin ciki ya ziyarci zuciyar shi a lokacin Kamar wanda akabawa sabon rai a ranan, sai cewa yayi Safiya har zaki koma ke nan tun yanzu ? Barin sa driver yazo ya kai ki ko ? Safiya tace ai da ka barshi kawai zan hau mashin, Maryam wace tasan kwana. Zancen hawa mashin din, Yace no, no no bari kawai yazo ya kai ki dama wanan zuwan nazo da security da yawa, Bai fi minti biyu ba sai ga wani yana sallama a waje haka maryam naji tana gani safiya ta wuce ta bar ta da sunan zata dawo gobe, Yusuf wanda yana ganin tafiyan Safiya din sai yayi tsaye yana kallon maryam Wace ke zaune tana wasa da yatsun hannun ta ta harde hannayen ta wani cikin wani, a lokacin, Kunyan Yusuf ya hanata motsawa daga inda take zaune, Batai aune ba sai ganin Yusuf din tayi kusa da ita zaune, Wani irin shu,umin murmushi yake sake mata Cikin wata irin murya yace maryam tawa zo mu shiga daga ciki ko ? Jukin maryam din ne yai sanyi, ji tayi duk wani irin kasala ya lullube ta, Tunanen abinda ya faru a tsakanin su daren jiya ya fado mata a rai, a hankali ta dan lumshe idon ta zuciyar ta ya shiga rawa, Tunanen ya zo mata wai yau ita maryam ce tare da Yusuf a matsayin mijin ta Muryan Yusuf taji yana cewa wai har yanzu maryam bazaki daina wanan damuwar ba, Ki sake ranki da ni maryam ki daina wahal min da zuciyar ki, hakanan, Hannu ya mika mata alamar tazo gare shi maryam wace a yanzu bata da zabi sai hakan ta dan mike a hankali zuwa gare shi, A hankali ta tako zuwa gare shi inda ya riko hannun ta ya ka mata zuwa jikin shi Rugumay ta yayi tsam yana mai sauke numfashi gudada , Sai kuma yadan dago ta yana kallon ta duk yadda yaso su hada ido dashi maryam ta kasa, Wani irin kallo yake mata shi dai a duniya kallon maryam bai isan shi , Komai nata sha,awa yake ba shu tun tana karaman ta, Daban yake kallon maryam din da sauran mata,,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [5/4, 7:09 AM] ‪+234 703 055 6607‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI KUNA MATUKAR SANI NISHADI DA JIN CIKAKKEN KARFIN GWUIWA YAN UWA , HAKIKA DOLE IN JINJINA MAKU GAMIDA GODIYA A GAREKU DIMBIM MASOYA NA NA ASALI, NAGODE NAGODE NAGODE KWARAI ALLAH YA BAR ZUMUNCI YAN UWA,,,,,,👏👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Kwanan su biyu a kwantagora yan uwa da abokan arziki suna zuwa taya su murnan aure Inda wasu ke cin su taran rashin fada masu da ba,ayi ba sai dai kawai suji labari, Kafin wani lokaci har labari ya karade gari mutane na cewa wai don kwadayi mahaifin maryam ya daura wa diyar shi aure da dan IBO tubabbe Wasu ma cewa suke yi da dan arne yai wa yar shi aure don kwadayin duniya, Wanan irin maganar yakai har zuwa kauyen da mahaifiyar maryam din ke aure, A,gidan buki wasu mata ke hiracewa yanzu ai duniya ta lalace ace mutun dan musulmai jikin musulmai don kwadai ya dauki yar shi yabawa dan kafirai, saboda kwadayin duniya, Aje a haifa wa mutun jikokin arna suzo daga karshe su addabi mutane da kafirci, Mahaiyar maryam wace,ke zaune tana sauraren su, Rayuwan ta ya baci a lokacin amma sai ta daure tankar bata san da su mutanen suke ba, Kishiyar tace ma taba da ansa da cewa ai musulmi duk musulmi ne, Shima bahaushe ai yare ne, don ba balarabe bane ai ko? Saboda ai larabawa sune tushen musulunci amma basu kyaman auren musulmi dan uwan su ko wani irin yare ne shi, Bayan sun dawo gidane abin yadamay ta don haka tafadawa maigidan ta duk yadda sukayi da mutanen, Wayan shi ta ara ya kira mata maryam din wace a lokacin tana zaune tana gyaran fruit, Ganin nomban mijin mahaifiyar tane yasa ta saurin daukan wayan, Cikin ladabi ta gaishe shi ya tambayi lafiyan ta tare da dan mata nasiha akan zaman aure, Ya mikawa mahaifiyar nata, inda tadauki wayan tana cewa yar baba ya kuke ya jama,an ku da sauran mutanen Ya maigidan naki yake, maryam din tana ansa mata da fadin lafiya kalau yake, Yar baba kiwa Allah ki bi mijin ki sauda kafa , yi nayi bari na bari, Kada ki bari komai yafito daga gare ki, duk halin da kika gani kiyi hakuri ki kokarta ki magance matsalar, Maryam wace tun tana cewa tau har takasa magana,sai hawaye dake fitowa daga idon ta, Nasiha sosai mahaifiyar nata tai mata tare da ja mata kunne akan maganganun mutane, Da bayan hannun ta take share hawayen dake gangaro mata a fuska, Daga,bayan ta taji an rungumota duk da tasan kowaye hakan bai hanata dan firgita ba, Wayan ya karba daga hannun ta ya gaisa da Inna din yai mata godiya inda yake sheda mata cewa zasu shigo gurin ta kafin su wuce, Maman ta daure tace mai kada su shigo yanzu yabari sai wani karon saboda yanzu ba,a dade da auren ba, Yai mata sallama inda take ta mai godiya da fatan alheri da gamawa lafiya da duniya, A hankali ya juyo da fuskanta zuwa gare shi suna fuskantar junan su Kamar wanda ke rada yake magana, bana son kina bata wanan kyakyawan fuskan naki da hawaye ki daina fitar dasu haka pls, Yadan kara dago da kanta ya kaleta yace maryam ina fatan muyi rayuwa da Insha Allah ba rabuwa a cikin ta, So kada zancen mutane ko wasu yan uwanki yatayar maki da hankali, Hannuwan nashi yasa yana mai goge mata fuska a hankali , Wani irin sha,awanta ke fisgan shi a lokacin, don haka a take idon shi ya canza kala, saboda wani irin mugun sha,awan mai sa kasala ke fisgan shi, Kamar may rada yace mata baki ce min komai ba maryam, Maryam din cikin wani irin murya wanda ke nuna karayan zuciya saboda tsoron ganin yadda idon Yusuf din ya sauya, alokaci guda, Tace insha Allah fatana ke nan , Fatan ki may maryam ? Yana mai kara matsota a jikun shi, Tace a hankali Insha Allah nace ba rabuwa ni da kai , Matseta yayi sosai a jikin shi kamar za,a kwace mai ita, Idon shi ya lumshe ya na sakin ajiyar zuciya saboda ko ba komai maganar ta yai mai dadi a rai, Sai yadan kallo ta yana mai daga kan shi sama yace, Godiya ya tabbata ga Allah ubangijin talikai, maryam har kullun zanci gaba da godewa Allah subbahanahu wata,ala A kan baiwar da yai min na mallakar mace kamar ki kamila,wace tasan may nene Allah da manzon sa suka ce, Kiran sallah magrib da aka fara yi shi yadakatar da shi inda yadan jaye ta kadan daga jikun shi yana mai lumshe ido, Bayan shi maryam tabi da kallo bayan gitan shi daga kitchen din, Tana mai ajiyar zuciya a filli, Wanan ne karo na farko tun bayan daura auren su da taji wani abu gamay da Yusuf din, Zaman kwana biyun da sukayi a gida guda yasa har ta dan fahinci kowaye Yusuf din, Shi mutum ne mai saukin kai ga kokarin ba natare da shi hakkin shi, Duk da dai sabon aure sukayi amma tadan fahinci yan abubuwa adangance da shi din, Itama gudun kada ta makara ta mike ta fada daki , Har ta idar da sallah ta zauna tana lazimi a gurin tare da yin tasbihi, Batabar gurin ba har Yusuf din yashigo yana dauke da basket din abinci da aka kawo daga gidan anty dije, Maryam din ce tamike tare da bin shawaran safiyan ta, Saman dining taka kulolin inda tai mai bissimillah cikin jin kunya da nauyi, Bawani abinci suka ci ba,sosai sun dai dan taba kadan, Wayan shi tai kara inda ta fahinci cewa da ma,aikatar su ne yaje waya, Mikewa maryam din tayi tsam tafara kwashe kayan da sukaci abincin zuwa kitchen, wanka ta fa da Inda tadan bata lokaci gurin gyaran jikin ta cikin bathroom din, Tana,zaune tana shafa mai da turare, dan gyara jikin irin ta mata taji motsin, shigowan Yusuf din, Bai wani bata lokaci ba,shima wankan ya shiga don kamar har yafi maryam din tsabta, ma, Daure yake da bathrobe a jikin shi yana kokarin goge ruwan jikin shi da dan karamin towel,, Yar jakar kayan da yazo da ita garin ya bude inda ya fito da kayan kamshin shi yakara gyara jikin shi tsab, Ta mirrow suka hada ido dashi ya wani dan kashe mata ido guda, Hakan yasa tai saurin dukar da fuskan ta a kasa Murmushi yayi kawai yaci gaba da,yin abinda yake yi, Batai aune ba taji muryan shi gab da ita yana cewa yau ina,son in cire wanan mugun kunyar da ake min wayo da,shi, Murmushi maryam tayi kasa,kasa saboda maganar da ya yi yana kallon yadda take wani takuran kan ta guri guda, Hannun ta ya kamo yana dan wasa da su can kuma ya dan tsaya yana kallon su kamar mai kallon wani abu a hannun, Daga haka ya fara canza sallon wasan nashi zuwa wani nau,in, Sosai ya canza mata sallon don wata irin mahaukaciyar soyayya ya ke nuna mata, Wanda bata taba sanin anayi wa mace ita ba, duk yadda maryam din yau taso ta kwaci kanta gare shi abin ya faskara so sai, Yakai wani lokaci manne da ita kafin ya sarara mata, Don haka yau ma a makare suka tashi don har an kusa tada sallah, Dasafe suna shirin komawa barci sai ga kira dole tafiya ya kana,su na komawa Abuja, Sai a,wanan lokacin hankalin maryam din ya tashi saboda bazata yarda da zancen bin shi ba, Abin da take sakawa azuciyar ta ke nan don haka ita ko a jikin ta shi kawai ke ta,shirin shi abinshi, Barci ya dan fara kwasan ta ke nan taji sallaman Safiyan ta, Dole ta bude idon ta da mamaki take kallon safiya din, Kafin ta kai ga tambayar ta sai ga Ànty Dije tare da yaran ta, Safiyace ke cewa maryam din wace zatai sammakon tafiya ce kwance abin ta, Cikin mamaki maryam ke kallon Anty ta tace aiba da ita za ai tafiyan ba, so may zai sa ta tashi yin shiri, Sai a lokacin Dije ta sa masu baki da cewa kamar ya badake za ai tafiyan ba, Zaman may zaki zauna nan din yi bayan mijin ki yana can shi, Ki tashi ku shirya ga safiya nan ,zata taya ki don shi tazo, Idon maryam ne ya kawo hawaye, a,lokacin amma sai ta daure bata bari ta zubo su ba, Badon ranta yaso ba tashi ta fara shirin Yusuf yacewa anty ba sai ta tafi da kaya ba don zasu saye a can idan sun tafi, Yan abubuwan sirin ta dawasu daga cikin kayan tada take so ta dauka, Maryam na gani tabar yan uwan ta da mahaifan ta da Anty ta da yaran ta, Aminiyar ta Safiya tana daga mata hannu duk kan su idon su ya kawo hawaye don rabuwa, Haka ma suka wuce garin mahaifiyar ta tana kallo babu daman shiga, Aure ke nan ta nisa a hankali don shi yakai can, Yusuf din ke jan motar da suke ciki da kan shi inda ya ke tuka su a hankali, Basu yi wani nisaba sosai barci ya dauki maryam din, Yadda yaga tadan kwantada kanta saman glass din motar sai ta bashi tausayi, Don yasan cewa tana tare da gajiya don ba karamin wahala yabata ba, a daren jiya, din, Yadan lumshe idon shi saboda abinda ya tuna a zuciyar shi, Sun isa gidan shi na Abuja lafiya inda ya yan aikin gidan suke ta faman yi mai sannu da zuwa, Babban falon gidan ne suka sauka inda sukaya da zango, Maryam wace sai kallon wanan gidan may kyauwo take yi a sace, Irin yadda masu aikin suka tare ta yasa maryam din jin dadi, Wani yaro ne ya sheko da gudu daga cikin gidan ya saye da,wata yar farar riga ga karamin wandon short niker, ajikin shi Yana cewa you are welcome my uncle, Daga shi sama Yusuf din yayi yana cewa miss u, my Pipkin, Maimata sunan maryam tayi tace a cikin zuciyar ta Pipkin, Da sauri ta daga kai ta kalli yaron inda ta ke mai kallon kurullla, ita ma,din, Yusuf wanda a yanzu ya rage dan tsawon shi daidai tsayin Pipkin din, Ya nuna ma Pipkin din maryam wace ke zaune a lokacin, Murmushi tasakar wa yaron da sauri, yaron yadan boye bayan Yusuf din, Ciin kunen Yusuf din yake magana a hankali yana cewa, Uncle who is she,? Yusuf yakara nuna maryam din yace she is your new Mumm, Go and greet her, A hankali yaron ya fara tafiya zuwa inda maryam din take, Kamar ba zai yi magana ba yace a hankali you are welcome mum, Jawo hannun yaron maryam tayi zuwa jikin tana cewa how are you Pipkin? Yana tafiya yake bata ansa da cewa iam fine, Murmushi maryam ta bi bayan yaron dashi don ganin cewa wai wanan yaron dan Naimat ne, Abin sha aka kawo mata tare da dan abin tabawa, Abinda hankalin maryam yafara kaiwa gare shi da farko shine ganin masu dan buje dake kai da kawowa agidan, Kalman nan da A,A yace ma don zata auri FUREN KAN, JUJI, Shi ya fado mata arai tana mamaki ya akayi duk irin son addini na Yusuf zai zauna da irin wa yan nan a gidan shi,? Wace yakira da,sunan NANI RUTH itace yace takira mai wayan nan masu aikin gaba dayan su, A gaban shi suka tsaya acikin natsuwa inda ya gabatar da Maryam gare yace masu matar shi ce, Daga yanzu itace matar gidan don haka duk wani tsari yanzu ,daga gareta zai fito, Suka ansa da fadar yes sir tare da kai kallon su caaa ga maryam din wace ke zaune cikin kamala da mutunci, Duk da karamace amma sai ta cika masu ido, Yusuf ya umurci Nani Ruth da takai mata kayan ta dakin dake facing din nashi na Pipkin, Da saurin ta ta wuce dauke da dan trolley din da yan kayan maryam ke ciki, Wanka tayi daga can ta dauro alwala tare dashirin gabatar da sallah don azahar har la,asar duk ya wuce su, Bayan ta idar ne tadan tashi takara bin dakin da kallon dakin acan acan, dashi yai mata kyau sosai, sai dai tana ganin yai mata girma ita kadai, Kofan dakin aka turo Yusuf ne wanan karon shima yai wanka ya sauya kayan shi zuwa wasu fararen simply material na maza, Inda take ya karaso fuskan shi dauke da murmushi , Matse ta yayi ajikin shi har sai da yaji ta sauke numfashi ajiyan zuciya sanan ya,sake ta, Bakin gado yaja hannunta suka zauna, yadan daga kai ya kalli dakin yace maryam wanan shine dakin ki da fatan zakiyi manage dashi kafin in samu time ai maki gyaran yadda ya kamata, Kallon shi tayi har yau acikin jin nauyi tace babu wani gyara da za ai yi anan is ok hakan ma, ai, Hannu ya daga mata yace Nop is my responsibility in gyara maki komai kamar yadda nai alkawari, Don haka maryam din bata kara cewa komaiba sai cewa da tayi, nagode a hankali,,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA,,,,,, [5/4, 7:10 AM] ‪+234 703 055 6607‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣1⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA,,, YAURI RAMADAN MUBARAK MASOYANA ALLAH YA SADA MU ALHERIN DA KE CIKIN WANNAN WATAN MAI ALBARKA ALLAHUMA AMEEN 👏👏👏👏👏👏👏👏 Kwanan su biyu da zuwa Abuja inda maryam a hankali take kara tantace sauki hali irin na Yusuf, wanda sam bai dauki duniya da zafi ba shi, Balaifi a gurin yan aikin gidan ma suna mutun ta ta kamar yadda ogan su ya umurce su da yi, Pipkin dai ne har yanzu bai yarda da ita ba don ko da yazo gurin uncle din shi bai kula ta, Yau ya kasance Monday don haka Yusuf da wuri yabar gidan zuwa office, Don tun da sukazo ba wqni abinda ya shiga tsakanin su saidai yana kula duk wani moved na ta a gidan, Sai da tai barcin ta tagaji ta tashi tadan yi wanka, Atamfane ajikin ta dinkin buje da riga masu ruwan, dark blue da yan adon farare kadan, A yadda taga table din alama ya nuna cewa ba wanda yaci abinci a gurin, Pipkin ne ya fado mata arai tunda taji uncle din shi nacewa ba school suna hutune, To ya akayi har zuwa wanan lokacin bai ci komai ba, Tsab maryam ta mike daga inda take zaune ta nufi dakin yaron duk da dai bata taba shiga ba, A hankali ta tura kofan dakin a yadda taga dakin ba laifi komai neat amma kuna dakin yana bukatan kara tsaba ta shi, ga idon ta, Har zata juya don a ganin ta bakowa adakin sai taga kamar ana motsi a cikin blanket din da ke saman gadon, A hankali ta isa har gurin muryan yaron taji yana cewa iam testing, Subbahanallahi marya tace da sauri ta yane bargon inda taga yaro kwance ya dunkule guri guda yana rawan dari, Hannun ta takai ga goshin shi taji wani irin zafi jikin shi radau, Rudewa tayi da farko amma daga baya sai ta tuna cewa su Assalam idan suna ciwo kusan itace mai dawainiya da su, Bathroom tafada na taga dan towel din yaron shi tadauka ta jika da ruwa ta matse shi sama sama, A hankali ta cire mai rigan jikin shi tafara dan goge mai jikin a hankali tanayi tana taba temperature din shi, Wani irin ajiyan zuciya taji yayi sai a lokacin ta tuna cewa bai ci komai ba Sauka ta yi inda ta koma falo ta hado mai ruwan tea mai kauri, bada bread ba, Daga kwance tawanke mai bakin shi tada shi zaune a hankali, Mika mai cup, din tayi inda tace mai ya bude bakinshi, Yaron ya ce, ba zai sha ba cikin kada kai, a hankali maryam ke lalashin shi har yadan sha rabin tea din, Maryam ta dauko wani riga ta samai sai a lokacin take tunanen ko ina nani din shi ta tafi har tabar shi cikin wanan halin haka, A hankali ta sauko zuwa, kasa hanyar da take tunanen shine kitchen, Can tagan su zaune wasu na aiki wasu na gulma, duk da tasan cewa gulman akanta ne, Suna ganin ta duk sai suka dan rude kowa da irin gaisuwan da yake mata, Cikin turanci take tambayar da tun yaushe ne Pipkin baida lafiya, Cikin faduwan gaba yar matashiyar ta dafa gaban ta tace Pipkin o, woo my goodness Maryam takara jefo mata tambaya ina maganin shi suke, Maimakon taba da ansa sai kuma ta kwasa tai sama da sauri, Itama maryam din bin bayan nani din tayi zuwa sama din, Ganin yadda maryam tai mai har gyara yaron yasa ta cewa cikin rudewa, iam sorry ma, Maganin maryam takarba da kan ta tabashi cikin hikima da basira har yaron yasha, Can ko a kitchen bayan fitar maryam din sauran yan aikin biyu dama su mata ukune ke aiki a gidan. Da ita nani da mai goge da gyaran gida sai wace ki girki, Bayan sun bita da kallo suka hada ido small girl, sukace a lokaci guda, Gudan cikin wani ya tsune fuska take magana , I wander how Oga managed marry dis girl, na Small girl woo, How she go do with oga ? Sai suka sa dariya, dayan tace Na because of her beauty woo, Beauty for where dis girl ? A,a na jealous you dey do D, girl look fine, woo She is moderate, Sai wace ke maganar banzan mai gyaran gida ta wani irin tabe bakin ta wai ita takaici Sosai ranan maryam ta kula da Pipkin wanda daga kwance yake kallon yadda ta kara gyara mai daki, Yarone karami amma sai ji kawai matar ta kwanta mai a rai, YUSUF yana zaune a office din shi maryam ce ta fado mai a rai saida ya wani lumshe idon shi tukun sanan ya furza iska daga bakin shi, Dagowa yayi daga kan computer din da yake aiki,, Kan shi ya mayan saman kujera yana dan juyawa a hankali, Irin surar halittan maryam din ne ke masa gizo a idon shi, Komai nata kamar ita taiwa kanta, anmata shi wadatace, Ga ta yar black beauty, da ita ga suma har baya ga dukiyan jiki ta ko ina Allah ya,wadatar da ita shi, Wayan shi yajawo saboda yana da bukatan jin muryan ta aima yayi kokari don rabon shi da ita tun a Kwantagora, Saboda yana tausayin kada ya wahal da ita don bata saba ba sai a hankali don ya kula da cewa indan ya kasance da ita, tana wahala da rana, Wayan maryam din na ringing amma bata daga ba , Lokacin tana bathroom din Pipkin tana mai gyara, Fitowan ta cikine daidai lokacin da kiran ya katse da sauri ta isa gurin amma kiran ya koma miss call Ganin nomban wanda yakiratane yasa ta maida kiran shi da sauri, Yadauka tare da ajiyan zuciya yace Maryam kina ina haka har hankalina ya tashi, Sai da tai murmushi sanan tace ban komai ina gurin Pipkin ne yau baida lafiya. Dam gaban shi ya fadi don bai son abinda ya taba yaron sam, Sai yaji muryan maryam na cewa amma yaji sauki har yayi barci ai, Ina ita nani take da zata bari kina wahala, bana son ki na wahala, da kanki, Ki kwanta ki huta komai ayi maki bana son ki dinga komai maryam, Iyakarki ki kwanta ki huta ki kunna A C , Maryam wace ta ke sauraren shi tun fara maganar shi, Sai yanzu ta katse shi cikin murmushi, da cewa uncle nifa mace ce dole dole inyi hidimar gida,. Ya no, no, maryam hidimata, na kawai zakiyi doni ne kawai dolen ki a yanzu, Amma ai hidimar Pipkin kamar naka ne ko ? ta tambaya cikin son jin ansa, Ya girgiza kanshi kamar tana ganin shi yace mata, No" may ye amfanin Nani din shi, Maryam ni banda ra,ayin matana tai aiki alhalin Allah ya hore min abinda zan biya don ki huta kamar yadda Allah yace, Kawai aiki gudane daga hidima na sai ta daukan ciki idan Allah ya kawo, Wani irin kunyane ya kama maryam din don dole badon taso ba takatse layin kiran, Murmushi yayi don yasan kunyar maganar taji, Don haka yasan maganin ta zai yi kokari yacire wanan kunyan gaba daya very soon, Ta gama shirinta tsab jira kawai takeyi gari ya waye basai ta fadawa jikan nata cewa tana hanya ba, Duk wasu yan tsaraba da ya kamata ta,saye ta saye a lokacin, Zaune take asaman wani benci dake a gidan ta, Tunanen mafarkin da tayi da jikan nata takeyi wanda takasa gane ko may hakan ke nufi Saidai mafarkin yana nuna mata cewa wani abin alheri ne zai samu Joseph din, Nan ta fara rero adduoi a cikin harshen yaren IBO tana mai yi wa Yusuf din addua, Rashin shirin shi da mahaifinshi yana damun yar tsohuwar sosai don tasan irin weakedness din Mr Ema din, Yan kabilan su ko acikin IBO riko gare su kamar bafillacen mutum, Ganin karfe shidda na marance yayi yasa maryam din yin wanka dongon riganta wanda Yusuf ya taba bata shi tasa Rigan yakarbi jikin ta yai mata kyau ta gyara daure kan ta da ribon yafitar da ita tsab, Waya Safiya ta bugo mata tana yi mata murnan yau satin ta guda cif a gidan Yusuf din, Saida tadan ritse idon ta tadan hade wani irin miyau sanan tace cikin yar siririyan murya, Nagode safiya kema Allah ya mayar a kanki yadda kikai mu Allah yai maki fiye dashi, Safiyan sai,da taji wani iri a zuciyar saboda ko ba,a fada tasan cewa aminiyar nata tana a cikkin sa,a, Bayan sun gama,wayan ne da safiya maryam tadan lumshe idon ta ita kadai tasan abinda take tunane a lokacin, Hakan ne ya hanata sanin cewa Yusuf din yadawo gidan har ya shigo dakin nata, Idonta a lumshe ta shako kamshin turaren shi a hancin ta Jin kamshin nashine yasa ta gane cewa Yusuf din yana kusa da ita alokaci, Bude manyan idon ta yi don ta ganewa idon ta ko hasashen ta gaskiya ne, Yusuf dine sagale da jacket din shi a wuya sai yar brief case din shi baka dake dauke a hannun shi guda, Hannayen shi ya ware mata yana cewa Are you thinking of your husband, ? Iam here for you, Ganin yadda ya ware hannayen nashi yasa tagane manufan shi, Don haka bata tsaya jiran komai ba tamike zuwa gare shi, Maida hannayen shi yayi ya rugumay ta ajikin shi suna shakan numfashin junar su, Don kan shi ya gaji ya sake ta yana cewa I miss you my beloved wife,, Yar case din dake hannun shi takarba tare da dan rusunnawa ta ban girma, Ta juya inda yake binta a baya zuwa part din shi yana kallon bayan ta da yadda take tafiya ta acikkn natsuwa wanda ke kara mata aji, Suna isa kofan dakin nashi ta ja ta tsaya a bakin kofan, Hakan yasa shi shima tsayawa kamar yadda tayi, Dago kai tayi tana kallon shi amma bazata iya jure abin da tagani ga idon shi ba don haka tai saurin dukar da kanta kasa, Tana kokarin mika mashi case din nashi a nufin ta yashiga dashi, Da hannu ya nuna mata su shiga dakin ba musu maryam din ta tura kofan dakin, Sai taga kofan dakin ya bude ga mamakin ta arufe dakin yake, Yusuf wanda rashin mussamai da maryam batayi akan duk abinda ya bukace ta dayi yasa shi kara son ta a ran shi, Maryam wace ta tura kofa taga ya bude, Amma sai gashi yabude ke nan kofan a bude yake barin shi? Kusan tare suka shiga dakin don haka batai wani daga kai takalli ko ina na dakin ba, Wani sanyi da kamshi ne suka cure guri guda,suke bada wani irin yanayin shaka alokaci guda, Saida hakan yasa maryam cikin wani irin yanayi mai wahal da zuciyan duk wani matashi mai lafiya, Saman gadon ya fada da karfi yana cewa wassh Allah na, Idon shi a rufe sai jin hannun maryam yayi tana zare mai takalmin dake a kafan shi har zuwa sock's din shi, Wani irin dadi yaji a zuciyar shi har takai ga ya lumshe idon shi, Bathroom tanufa ta hada mai ruwan wanka, ta aje mai toothpaste a gefe guda gami da towel, Ko da ta fito yana zaune a bakin gado yana balle bottoms din rigar shi a hankali, Maryam ta hango gashin dake kwance a saman chest din shi, Cikin sauri ta kawar da kan ta a gefe guda don bata taba ganin namiji acikin irin wanan yanayin ba, Kizo ki kara sa tube min maryam duk na gaji, wallahi, Batai magana ba,sai ganin tayayi ta nufi hanyar fita wajen dakin da sauri, Sai da takai kofa tace idan kagama abinci yana a kasa, daga haka tabar dakin Murmushi yayi bayan fitar ta don yasan cewa shi ko a hakan ma yagode mata ai, Wanka yafada yi bayan yafito ne a cikin shirin ya nufi dakin Pipkin zaune ya samay su da maryam ta na ba shi fresh milk a wani dan farin cup na glass, A yanayin da ya gan su yaji dadin hakan sosai don dai bai tsanmaci hakan ba da sauri, Shikan komai na maryam din a sauki yake zo mashi a rayuwa, Daga nan suka kwasa zuwa dining don cin abinci, Ana budewa yaga favorite food din shi ne yakuma san cewa ita mai aikin shi bawai tasan abinda yake so bane, Sau guda yakai a bakin shi yadago kai da sauri ya kalli inda maryam take zaune, Ido ta lumshe mashi tare da kada mai kai tana mai alamar eh, Sosai ya kwashi abincin yau hankali a kwance yaci ya sha ruwan zobo da ta hada masu, Ranan daga massalaci babu inda Yusuf ya kara zuwa bai fita ki ina ba kamar yadda ya saba, Karfe tara na dare maryam a dakin ta zaune tana dan gyare gyaren su na mata, Dukawa yayi daidai da tsayin da take zaune yadan rankwafo mata Maryam duk da na hanaki aikin komai saida kika shiga kitchen ki kai aiki, Matsota ya yi zuwa jikin shi yace nafada maki aikinane kawai matsalar ki bawai na gida ba, Amma tunda kina son aiki ne bari yau in gwada sa,a ta ingani ko zanyi sharp shutter, Sai ya hado kan shi da nata guri guda ya kai mata kiss, a goshi, Daga haka ya mike ta tsaye yana kokarin kai hannun shi a kirjin ta, Kunya ne ya kama Maryam din cikin sauri ta kwantar da kanta so,sai a kirjin shi, Daukan ta yayi cak tare da kashe wutan dakin zuwa dakin shi, Cike da shagwaba muryan maryam din tace haba dai uncle don Allah ka saukeni inyi tafiya mana, Wani irin kallo yabita dashi wanda yasa ta noke kai cikin kirjin shi,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [5/4, 7:11 AM] ‪+234 703 055 6607‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣2⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI JAMA,ATUL MUSULMI,NA RAMADAN MUBARAK 👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Hasken ranan da ya bullota glass din window dakin shine ya farkan da Yusuf din wada ya zabura da karfi yana fadar subbahanallah, Maryam ki tashi mun makara ga sallah yau, cikin saurin ya sauka saman gadon, Maryam wace jikin ta yai mata tsami tai mika itama dai, cikin kalman sunan Allah tai istigifar na makaran da sukayi, Ko da Yusuf din ya fito bathroom din Maryam din bata dakin don haka yata da,sallah shi kawai, Gurinda ya zauna yake lazimi nan yake tunan cewa tunda ya musulunta bai taba latin sallah ba Amma yanzu tunda maryam tashigo rayuwan shi sai gashi yana son yin wasa da ibadan shi, Itama dai maryam a dakin ta bayan tai wankane tana zaune tana shafa mai take irin wanan tunanen tarasa may ke jawo mata wanan lazyness din haka Kitchen tafada inda taimai simply breakfast da kanta , Tana tsaye a gaban dining table yafito cikin shirin shi na fita office a gaban table din ya hango ta, A hankali ya karaso gurin da take yana kokarin jan kujera ya zauna ne maryam din ke ce mai ina kwana cikin girmamawa, Hancin ta yalakato yana fadin bakya jin magana ko duk da gajiyan dake jikin ki sai da kika shiga kitchen ko? Cikin dan marairai ce murya maryam din tace ina kwadayin ladan aure kamar ko wace salihan mace, Wani irin kallo yai mata yace cikin kashe ido banda ladan da kika kwasa a daren wani lada kuma kike bukata, Jawota yayi zuwa jikin shi yana cewa ke fa maryam nagane cewa wayo kike son kimin duk ki kwashe ladan ke kadai, Kokarin lalabanta yakeyi amma sai maryam din ta zille mai Murmushi yabita da shi yana cewa ai satin nan yana karewa zamu fita honey,moon din mu Nagaji da wanan wayon da ake min kullun nima inason yin aikin lada, koya kikace yakare zancen yana daga mata gira, Murya kasa kasa maryam tace uncle kaci abinci kada ka makara pls, Sai da yadan lumshe idon shi yace, wanan duk sallon wayo ne kikadauko ko maryam don kar na more safiiyana ko,? Saida maryam ta tabbatar Yusuf din yafita cikin dadin rai da godewa sanan ta koma kan Pipkin shima komai na shi tsab ta tab batar da yaron yai wanka, yasha maganin shi, Sanan ta koma dakin ta wanka takarayi tasa wani dogon riga ajikin ta mai dan guntun hannu kwantawa tayi don ta rama barcin jiya dake idon ta, Don daren jiya Allah ne kawai ya kwato ta a hannun yusuf din wanda bai raga mata ba kamar ba gobe, Barci mai nauyi tayi ba ita tafarka ba sai gaba da sallah azuhur, Bayan tai wanka tafito ne ta gyara jikin ta, abincin safe da ta,aje shine ta tafi dauka don taci, Saboda dai ita gaskiya bazata iya cin abincin wa yan nan masu dan bujen ba da kai a sake, Tayi iya kokarinta tun zuwan ta don ta tursasa zuciyan ta taci abincin su sam ta kasa, Hakan ma na daya daga cikin abin da yahanata tsayawa yin bakunta ko ko bin nauyin jiki tafara girkinta abin ta, Pipkin ne ya fado mata arai don ya kamata yanzu ta fara koya ma taron addini a hankali, Sai kamshi take yi inda tafito dakin ta zuwa dakin Pipkin din amma baya ciki a lokacin, Don haka ta tako zuwa kasa don ta diba ko yana can don alama ya nuna cewa yaji sauki ke nan, Guri guda taja ta tsaya takasa karasowa zuwa cikin falon, Don ganin yar tsohuwad da tayi zaune ta murtuke fuskan ta babu walwala ko kadan atare da ita, Kamar ta koma sai dai ta daure ta kara sa cikin falon, A hankali ta isa har gurin da maman Choima din take zaune cikin matsanacin bacin rai, Gefen ta ta isa inda ta durkusa har kasa kasan ties take ce mata cikin ladabi, You are welcome ma, Maryam ta karasa kai zaune a gurin taci gaba da gaida tsohuwan wace alama ya nuna cewa yar uwan maigidan ne, Tsohuwan na zaune da wani zanin jugei ta aza wani saman wani kanta babu dan kwali sai dai duk an aske gashin kan, Pipkin wanda ke kwance gefen tsohuwan yana danan game din shi jin muryan maryam yadan sashi dago yace, Grandmother dis is my new, Mumm, Buge mai hannun da yake nuna maryam din tayi tana cewa cikin yaren IBO kada yakara fadan hakana agaban ta, Wani irin mugun kallo ta,watso ma maryam din wace ke zaune a kasan ties, tana dan wasa da yatsun hannun ta, Mikewa tayi ta shiga kitchen ganin cewa kusan lokacin fara girkin marance yayi , Amma kuma sai ta tuna da cewa bata ba wa wanan tsohuwar ruwa ba don haka ta shiryo su a ture ta kawo mata ai wani mugun kallo ta,watsa mata, Ba,shiri maryam ta bar gurin batare da ta kwashi kayan ba a nan tabar su, Abinci irin na gargajita ta hada masu, tuwon semovita da miyar agushi yaji nama gudun gundun, naman ya nuna da kyau, Sai ruwan shayi da ta dafa da kayan yaji saboda tadan yi nazirin maigidan nata ma,abuci shan shayi ne shi, Kamarya yadda tasan Anty ta dije tafison sarrafa zobo a nau,i nau,i ita ma dai maryam din hakan ne don ta hada masu zobo da kankakana , Kafin wani lokaci ta hada komai ta gyara kitchen din Ta koma dakinta ta shirya jikin ta tsab cikin wani dogon rigar atamfa din kinshi mai matse jikine sai hannu shara,shara da akai mai, Daidai lokacin taji horn din motar maigidan a wajen gidan, Takowa tajeyi daga steps din a hankali inda hakan yai daidai da shigowan shi gidan, Ga maman Choima zaune yana mata sannu da zuwa ga kuma maryam black din shi tana saukowa daga steps, Kamshin jikin ta har zuwa gurin da yake tsaye , Cikin daurewa da matsewa ya dan je gurin tsohuwan wace ke kallon mamaki, A lokacin ne maryam ta karaso gurin tana mai sannu da zuwa cikin yar makkan murya, Barin tsohuwan yayi ya riko hannun maryam din yadan kai mata kiss riko ta yayi zuwa jikin shi yana cewa Mama meet my beautiful wife maryam she is hausa fulani by tribe, Sai kuma ya juya gurin mraryam ita da hannun yace mata dis is my grandmother, My mother, mother, Dan kara rusun,nawa maryam din tayi cikin girmamawa tace you are welcome mama, Sai yaji dadin yadda tayi batare da nuna wani kyama ba a yadda maman tazo da kai ko dankwali babu, sama, Jakar hannun shi ta karba inda ta juya tabar su nan a tare, Dakin da Grandma, take Maryam da kanta ta kara gyarawa, Ita ko sai wani ya mutsa fuska takeyi wai tana jin haushin Maryam tare da,jikan ta, Abinci so sai su ka kwasa don kowan su har Pipkin yaji dadin wanan girkin, Maman choima ce ke tambayar ya canza mai masu girki ne halan ya girgiza kan shi lokacin da yake wanke hannuwan da ruwan da maryam ta ahe mai a gefe don wanke hannayen su, Washegari Yusuf bai fita zuwa gurin aiki ba yana gida manne da yar amaryan shi yana morewa, Wanan yinin haka Yusuf din yakoma masu kamar wawa agidan don yna manne da matar shi, Cin abinci kawai ke fitar dashi waje don kar ya zauna da yunwa, Sai zuwa karfe shidda saura yabar gidan yana saye da wani wando cryzy fari da bakin tie shirt mai yar wuya,round, Wani katon super market ya tafi inda ya sawo masu kayan bukatan gida,, Daga ciki kayan maryam yafi yawa saboda yasan tana da bukatan su, Yaso da sai sun tafi waje ne yai mata lefen ta a can, Yasan tabbas maryam takai yar albae Amma kuma yanzu fitan su kasan zai dan dauki lokaci saboda shigowan grandmother, A,falo ya samu Grandma tare da, Pipkin, suna kallo maryam tana,dakin tana lazimi don anyi sallah magrib, Grandma tabi ledodin da ido don gano ko may ke a cikin su, Ukeria, mai masu wanki da guga shine ya shigo gidan da kayan wanda tun can ogan shi ya fada mai cewa ya kai sama gurin madam din shi, Yana ajewa shima Yusuf din yana,shigowa da,wasu, Maryam ta tofa adduan gami da shafe jikin ta dashi tadan dago kai tana cewa maigidan nata sannu da zuwa, Sai kuma yakai kallon ta ga kayan fuskan ta taf da tambaya, Shida kan shi ya zauna yana fitar da kayan tare da yi mata bayanin cewa yan kayan da,zata fara amfani dasu ne ya,siyo mata don tafiyan su ba yan zu ba Idan kuma akwai wasu abinda take so sai ta fadi a sayo mata, Da sauri maryam ta dago kai ta kalle shi tace wanan ma,sun isa basai an karo ba nagode kwarai tausayi tabashi saboda ganin dan abin da yai mata amma tana mai irin wanan godiyan da addu,a, Bayan ya fito ne ya ga wani irin kallon da maman Choima taimai direct gurin ta ya nufa saboda bai son ace, za,a samu matsala daga gurin ta, Hannun tsohuwan yariko yace mata cikin yaren su yana son taso matar shi kamar yadda take son shi, Kafin yaci gaba tai wani irin daga hannuwan ta tazagoyo da su takan ta tace, Over my death body, To love dis awsa girl never, never, Murmushi yayi ya mike ya na cewa mama I don't want to have problem with you, Juyawa tayi tana fada acikin harshen yaren su tana cewa, ita sam sai ya sallami maryam din tabar gida Dariya maganar taba Yusuf saboda yasan kafirci yasa kakan nashi fadin haka, Su Jibrin ne da KB din suka kawo masu ziyar da daren yau, A gidan suka ci abincin dare tare da su amma banda maryam wace ke Ciki bata fito ba don kascewar su baki maza, Sai bayan sun gamane maryam din tafito cikin wani dogon riga har kasa rigar yai mata kyau sosai Tana saye da wani dan hijab a saman shi wanda iyakar shi iya kafadar ta,. Da murmushi a fuskan ta don ganin su da tayi tankar a gida kwantagora take, Su ko su Jibrin sai kallon yadda maryam din ta canza cikin dan lokaci guda sukeyi, Shiru tadan yi inda su ka ci gaba da hiran su a tsakanin su, Maryam din ce ke tambayan Jibrin labarin Safiyan ta, Saida yadan kalli su KB sai ya kwashe da dariya yace maryam ai kin,fi kusa da safiya yanzu Mamaki maganar Jibrin ya ba maryam din don maganar ya daure mata kai, Yusuf ne ya gane cewa maryam tadan shiga rudu a cikin maganar tasu, Sai KB ne ke cewa Yusuf ai ya bar matar shi ta kusa haihuwa don haka ba zai dade ba zai koma KG din, KB nawa yusu hra shiko Yusuf duk hankalin shi na gurin rabin ran shi maryam, Yusuf ne ya jefowa Jibrin tambaya don dai maryam ta fahinci zan cen shi , Tambayan Jibrin yakara yi da cewa yaushe ne wai zancen auren ku kai Jibrin da Safiya, Nan ma dariyan yayi sai da yadan numfasa sanan yace wa Yusuf din gaskiya maganar nan tamu tana rawa ne yanzu, Da sauri maryam tadago idon ta ta sauke su ga Jibrin cin don gaskanta zancen sshi Pipkin ne ya katse zancen don ya sauko da gudu nani tana bin shi a baya wai ya tsaya yasha maganin shi, Shiko sai tsala ihu yakeyi yana gan garowa, duk sai hankalin su ya koma gare shi a lokaci guda, Kuka yaron ke yi matyam ce ta karbi magani cikin hikima ta bashi yasha, ta dauko ruwa taba shi ya kara kurbawa, Hakan ya burge kowa dake gurin don daga haka tajawo yaron zuwa cikin jikin ta shiko ya lafe,abin shi, Tun wanan lokacin Yusuf bai gane kan maryam din ba badon komai ba sai don maganar da Jibrin din yayi akan aminiyar ta, Tana zaune bayan ta samu ta lalaba Pipkin yai barci shine tadan shiga bayi tawatso ruwa, Ribon take kokarin kama kan tada shi guri guda, Yayin da taji hannun Yusuf din akan, ta, ido suka hada daga cikin mirrow da Yusuf din, Ribon din yakarba a hannunta, ya daura mata shi tsab a kai, Gaban ta yadawo ya tsaya inda yadan jingina jikin shi da mirror din da take kwalliya akai, Sunan ta ya kira a hankali , Ita ma ido tadago ta kalle shi cikin jin nauyi kamar kullun, May kika fahinta akan zancencen Jibrin a Safiya ne, ? Murya narkarka kamar mai shirin kuka cike da shagwaba maryam din tace , Gaskiya uncle ina ganin kamar akwai rikici a tsakanin su saboda tun ina gida na bar jin Safiya tana zancen Jibrin din, Yusuf ya funkule hannun shi guri guda yana dan bubuga su cikin juna, Ya lumshe idon shi ya bude su a lokaci guda ya dan furzar da iska waje, Zan sa a bincikar min dalili insha Allah,,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [5/5, 9:13 PM] ‪+234 703 055 6607‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣3⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI ADDU,AN NAKE NEMA AGURIN KU, DA FATAN ZAKU TAYANI ROKON ALLAH JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA RAMADAN MUBARAK👏👏👏👏 Yadda Yusuf yaga,cewa hankalin maryam ya kwanta da zancen da yai mata, Bayan shi maryam tabi da kallo ta re da sauke ajiyan zuciya, Mikewa tayi zuwa gurin window dakin, tana kallon furannin dake haraban gidan, Zuciyar ta na cigaba da harbo mata maganganun da Jibrin ya yi daren jiya, Abinda ya faru abayane yazo mata sabo fill yadda yai ta magiya akan tai ma safiya din magana, Don irin yadda Jibrin din ya rude da akan samun yardan safiya taso shi a lokacin da yafara son ta, To may yafaru haka a tsakanin don dai tasan cewa kowan su na son dan uwan shi, Innalillahi wa,inna ilaihi raji'un" Maryam tai saurin ambato wanan kalman a sarari gami da rintse idon ta, don dai tasan da akwai matsala Idan ko hakane Jibrin din yaci amanar aminiyar nata ke nan, don dai itace silar hada su , Tana cikin wanan tunanen ne tsaye a bakin window taji muryan Pipkin a kusa da,ita, Murmushin dole maryam ta kirkiro tace cikin turanci Pipkin ina nani batai maka wanka ba, Hannun yaron takama zuwa dakin shi inda taimai wanka ta shirya shi, Abinci taba shi yaron ya bude cikin shi yaci sosai ya kwashi abin cin, Maman Choima fitowan ta ke nan daga daki a falo tasamay su maryam din na gogewa Pipkin bakin shi, Wani irin ya tsune fuska tayi tawani kau da kai gefe guda, Maryam ta mike a cikin girmamawa tace a mama ina kwana a harshen turanci, Kamar bazata ansa ba sai can ta ansa da cewa lafiya kawai daga haka tafara kokarin hada abin kari, da kanta, Ganin Pipkin yana wasan shi yasa maryam mikewa zuwa dakin ta, Wayan ta ne dauko don takira Safiya, kira guda ga na biyu safiyan ta daga wayan kamar wace ke jiran wayan, Cikin tsokana suka fara magana, a,a mutanen Abuja ai da har nayi fushi. Haba dai inji maryam safiya tace amarci tun yanzu ya hana zumunci kullun na kira waya akashe, Murmushi maryam din tayi tana yar dariya ciki ciki, itace tafara kau da zancen sherin da Safiyan ke mata da cewa, Ya su mama da sauran mutanen gida Safiya tace wallahi suna nan lafiya kalau, Wai ko kin san wani abu, inji safiya take tambayar maryam, Nan da nan gaban maryam din yafadi dam don tana zaton maganar su da Jibrin ne zata fada mata, Safiya tace na je Kamfanin Bobi gurin mama, Cikin wani irin ihu maryam tace ke safiya dan Allah dai Safiyan ta ansa da fadar wallahi ko, Kwana na biyu a can wani irin dadi ne ya lulube maryam din takara jin son aminiyar nata, O, o safiya nagode kwarai, wallahi, da sauri safiya tace may na godiya aciki ina nima uwatace mama din, Murmushi maryam ta yi har safyan taji hakan a wayan ta, Nan dai safiya taiwa maryam labarin irin dadin da taji gurin mama din, Anty Dije fa inji maryam tana tambayan safiya , Safiya taba da ansa a takaice da cewa ban je ba maryam, Cikin mamaki tace saboda may Safiya cikin sauri safiyan tace dalilina ne kawai bada wani ba, Haba dai safiya Anty n nawa zaki ki zuwa gidan ta akan may, Ke ya maigidan ki da mutanen ku duk suna lafiya ko safiya din ke tambaya tana son a wuce zancen Anty Dijen, Amma sai maryam din tace gaskiya nai mamaki kwarai da jin hakan safiya, Maryam ke bazaki gane komai ba don haka mubar zancen don. Allah ki ce ina gaida uncle don Allah, Dakata Safiya inji maryam din tace wai ya zancen ku da Jibrin ne don naji shiru ba wani zance akai, Shiru safiya din tayi can kuma sai ta dan nisa tace maryam kibar zancen Jibrin pls, Saboda may safiya maryam din tai mata takaitacen tambaya ? Maryam don Allah mubar wanan zance kawai dai na gode wa Allah da ba wani abinda ya shiga tsakani na dashi, Subbahanallah inji maryam abin har yakai cen amma ban sani ba Safiya, Maryam sanin baida wani amfani ne shiyasa ban fada maki ba tun farko , Ikon Allah safiya fada min tsakani da Allah may ya hada ku ? Maryam bawaini zance bane mai tsawo matsalan a,kankine kawai Ido waje maryam ta kara tambaya cikin daga murya tace matsala tafa kika ce safiya, Nashiga uku ni maryam tace cikin karayan murya may nayi har zan shiga tsakanin ku haka ? A takaice Safiya tace wai kin aurewa yar uwan shi saurayi har kuma da sheri kukai mata, Nan dai tafara ba maryam labari kamar haka, Watarana yazo gurina rai bace bai wani dade dazuwa ba a ka kirashi ga waya, Bayan ya daukane na fahince da mace yake magana Inda naji yana cewa wai aidama don haka ita dije duk ta asirce Yusuf din don ta hamdamay komai nashi, Hakan bai mata ba shine yanzu take kokarin hada Yusuf da kaunar ta, Haka sukai ta zancen har zuwa lokacin da suka gama, Bayan sungama ne nake ce mai may yafaru ne wai, bai boye min bayake shedazmin cewa wai ai kuna nan kuna tawa Yusuf kule,kule akan ya aure ki, Nan nake sheda mai cewa ke baki ko ra,ayin wanan hadin Yace wai inji wa ya fada min wai harda kazafi kukayiwa cousin sister shi cewa tana maki asiri, Safiya tace nan da nan rai na ya baci wallahi maryam nadinga mai nasiha akan shiga maganar mata, Sama sama muke dashi saiga zancen auren ku da Yusuf andaura shine yace wai ai har da ni a cikkin kulle,kullen da akayi, Wai ai sai ya rama wa ita sadiyan abinda Yusuf yai mai, Wai shima da yake tubabbe mara asali har zai, wa mutane rainin wayo, Ita ko sai tace mai aiko baida asali yana da abinda ke nemo asali ai don ko acikin rashin asalin suke bin shi har suna cin arzikin shi, Kawai kin san may hannu yadaga yakai min mari a fuska, Tun wanan ranan muka samu matsala yanzu naji ance wai shi zai auri Sadiyan ai, Maryam tace, O Allah ni maryam yanzu sakaiytan da Jibrin zai muna ke nan, Aikuwa wallahi shi yai hasara insha Allah indai don ya rabu dake ne zai auri sadiya yaje ganin kamar yai maki bakin cikine, Ke maryam ni wallahi nama fita zancen kinji nabarwa Allah zabi akai, Allah yai muna mafi alheri inji maryam din tafada rai a bace , Sun dauki lokaci suna tataunawa akai har maryam din ta fahinci cewa ba komai ai safiya din ta hakkura, Yinin ranan haka maryam din ta wuni rai a bace tana tunanen zancen Jibrin din,. Dan Adam abin tsoro ne gaakiya ya za,a ce wai Jibrin ne zai fadawa Yusuf irin wanan zancen haba dai duniya, Kara jin aminiyar nata tayi azuciyar ta saboda ita safiya ta,sadaukar da soyayyan ta, Ai yukan da duk ya kamata maryam din tayi na gida alokacin su tagabatar, Tadan ce bari tadan fita yau tasha iska a kasa don tun ranan da tazo bata taba fita wajen ba, Ta kofan kitchen din su wanda zai sada mutum da waje maryam din tabi, A kitchen ta hango markade a wuta amma bataga mai aikin aciki ba, Tana sa kafan ta a waje ta hango mai girkin nasu ta kware riga tana fitsari a tsaye can bayan flowers din su, Cikin sauri maryam ta dawo baya cikin rawan jiki gaban ta sai faduwa yakeyi a lokacin, Saboda ada labari take ji bata tabbatar da cewa haka suke fitsarin su da gaske ba, Nan take taji zuciyar na tashi don abincin da matar ta taba dafawa taci ji tayi kamar ta jawo shi, yafito, Dakin ta takoma tana mai jin wani irin juwa na kokarin kwasan ta saboda har falon nasu kazantan shi maryam takama ji, Zaune take saman gadon ta kafan ta zube daga kasan gadon bata hau dasu sama ba, Tayi zurfi a cikin tunanen abinda tagani da yadda zata kara tsayawa tayi rayuwa da su acikin gida daya a haka, Har mai gidan nata, ya dawo maryam bata kula da cewa time din shi na dawowa yayi ba, Yadan dade a tsaye gurin yana kallon ta hannun shi ya sa yadan gada gab da fuskan ta abinda yasa ta szurin yin ajiyar zuciya, Ta daga manyan fararen idon ta tadan kalleshi , da ido tace mai sannu da dawo wa uncle, Tana son tashi zaune, amma sai ya hanata mikewa zaune, din Ta hanyar dan kwanto mata daga tsayen, murmushi tayi ita ma tare da dan ware hannayen ta,,, Sosai suka murji junan su a lokacin ba karamin dadi Yusuf din yaji ba ganin ya fara,samun responde daga maryam din wace ada shi kadai ke gidan shi da rawan shi, Maryam wanka tafada ta gyara jikin ta kafin lokacin sallah ya karaso, Sai dai kuma bayan komai ya kammala tanemi damuwar da take ciki kan aminiyar ta tarasa, Jin zuciyar ta takeyi wani wasau dashi bakan dazuba matsala guda yanzu hanyar da zata tun kari Yusuf da zancen masu guntun bujen dake gidan dasunan yan aiki, Bayan ta idar da sallah a gurin da take zaune take tunanen yadda zata bullo ma wanan zancen na yan aikin masu fitsari a tsaye, Gashi bata,son ta fadawa kowa sirin gidan ta don irin wanan na a cikin kalman furen juji, Daga karshe wani shawara yazo mata azuciyan ta don haka ta yanke shawaran tunkarar shi akai, Saboda ko banza bazata so tazama silar hana cin abincin wani dan adam ba ,,,,, Falo shi na sama yake zaune bayan ya dawo daga massalaci, kira,a yasa wanda duk inda kake a gidan zaka iya jin sautin,shi, Cikin wani dongon riga da Yusuf yasayo mata maryam take rigar mai adon duwatsu har kusan kasan shi da wasu hannaye shara,shara tadaura dan kwalin rigan akan ta, Laptop din shi agaban shi dagani tasan aiki yake acikin shi Cup ne a hannun ta dauke da milk a cikin shi mai sanyi tasa dan wani marfi ta rufe, Falon nashi ba kowa ke shigowa cikin shiba in bashi da ita ba yanzu, Kusan yaune ranan farko da maryam din tafara samun shi a falon saboda ta fahinci cewa guri kamar inda yake samun natsuwa agida, Tunda ya hango tafe sai yaji ya kasa yin aikin dake agaban shi sai kallon shi ya koma gare ta Maryam wace tafe take acikin rausaya kamar zata karye don rangwada, amma ita batasan tana yi ba,,,, Yusuf a zuciya, shi sai hamdallah ya keyiwa Allah daya bashi maryam a matsayin matar shi, Haban shi ya rike da hannunshi kaman mai mamaki, Kafafuwan shi suna mike saidai ya harde daya cikin daya, Isowan maryam gaban shi yai daidai da sauke ajiyan zuciyan shi, Cup din milk din da takawo mai ta dan aje saman stol din da ke gefen kujerar, Mastawa tayi gab dashi tasa hannun ta ta cire mai hannun da ya tallabo haban shi dashi Idon shi ya zubo acikin fuskan ta cikin murya mai sanyi yace mata, Maryam a kullun na kasance tare dake sai in rasa irin godiyan da zan ma ubangijina da ya mallaka min ke a matsayin matar sunna na, Kalan shi maryam tayi cikin natsuwa ta sake mai wani irin lalausar murmushi, Don kokarin ta na isar da maganar da tazo mai dashi, Gashi tun agida tasha alwashin rike mijin ta da,zuciya daya akarkashin yina nayi bari na bari, Badon komai ba sai don cikawa mahaifinta burin shi na wanda shi kadai yasan dalilin bata Yusuf a matsayin mijinta Saman hannun kujerar da yake takai zaune tadan kwanto da jikin ta saman kujerar , Ta ce cikin wani murya hmmm uncle ni ban ce nagode ma Allah da ya nufeni da zama matar ka aduniya har nake fatan a lahiran mu , Cikin sauri yatare ta da cewa in sha Allah maryam in Allah ya yarda, Ameen ta ansa mai dashi, Uncle a yanzu fa kai ne mutum mafi daraja a wurina, Banda wanda yakai daraja a guna domin aljanna ta tana akarkashin kafan ka ne, Gashi a sannu ka koyar dani sonka acikin dan lokaci kankani, Banda wanda nake ji dashi nake son shi face kai mijina uban diya na ayanzu ban damu da duk wani abinda mutane ke cewa akan ka ba, Tunda maryam ta fara jero maganar ta bata tsaya ba sai da takai karshe, batare da ta tsaya jin may zai ce ba, Rugumota yayi zuwa cikin jikin shi saboda bai taba tsanmanin jin ko makaman cin wanan maganar daga bakin ta ba, Sai gashi yau ita maryam ce da kanta take fadamai da bakinta, Don haka zancen ya shiga zuciyar Yusuf sosai har takai ga ya kasa cewa komai sai binta da lalaba yake yi, Itako maryam dama abinda take jira kenan taga cewa ta birkita mai lissafin shi kafin ta fara aiwatar da plan din ta "Maryam! ya fadi sunan nata cikin wani yanayi sai kuma yaja bakin shi yai shiru ya kasa furta ko mai akai, Wata kila kuma don bai da kalman da zai iya fada ne a lokacin, Kara noke kanta tayi saman kirjin shi tace I love you uncle Yusuf, Tare da kai bakinta acikin kunnuwan shi ta furta mai hakan, Nan da nan jikin Yusuf din yadauki rawa tankar yau yafara sanin maryam din, Hakan yaba maryam daman yimai wasu abubuwan da bai ma san ta iya ba, saboda takara cusa kanta gare shi kamar yadda kowace mace ke kokarin yi don mallakan mijin ta gare ta, Lokaci mai tsawo suka dauka ita dashi acikin wani irin yanayi da ba zai yiwu a fade shi ba , Sannu a hankali maryam din ta dan fara zamay jikinta a cikin nashi, Ta koma gefe guda tana kokarin sauke numfashin ta, Sai a lokacin hankalin su yadan dawo suka tuna da gurin da suke Cikin sauri maryam din tafara mikewa tsaye tana kokarin gyara gaban riganta da ya bude, Sannan takai dan zaune saman kujera dake kusa da ita, Yusuf wanda ke kwance saman floor plat dashi daga shi sai yar tree quiter dake a jikin shi, Gyaran murya yayi yana miko mata hannu alamar ta daga shi daga kwancen, Dariya tadan kama mashi don sai a lokacin ta tuna da milk din da takawo mai, Cup din milk din tadauko tanufo shi dashi inda yake kwance tana cewa tashi ga milk kada yai sanyi baja sha ba, Idon shi a lumshe lokacin cikin kasala yadan kai zaune yajingina bayan shi ga kujera Bayan ta mika mai yadan kurba kadan sai ya lumshe idon shi, Azaton shi madaran ce sahihiyar ta sai da ya kurba yaji bambamci a cikin shi, Sald milk ne a ka hada wanda ke bada kamshin flavor mai dadi, Cikin lumshe ido Yusuf yace waya koya maki wanan hadin little Mum ? Sunan da yakirata yasata dan shiga wani yana saboda ya sa tatuna da abubuwa da dama da suka wuce, Mai makon tabashi ansa sai cewa tayi hmmm inji Assalam ko ? Gyara dan zaman ta tayi sanan tace Uncle dama ko ina son in dan roki wata alfarma a gare ka, Cikin mamaki ya dago kan shi ya kalle ta yace alfarman ke nan maryam, Don Allah so nakeyi a bude min kitchen dina daban sai in barwa su ukeria wancan din surika abincin su suda sauran masu aiki , Sai tai shiru alamar tana jiran jin ansar shi a lokacin, Shiru yayi yana kallon cup din milk din dake hannun shi kamar mai nazarin wani abu, Sai dayadan kara kuba milk din sanan yace ko so kike akoresu don banyi zaton zaki iya kai warhaka dasu ba don nasan ki da kyamar mara sallah, Kunya maganar tashi taba don dai yagano inda maganar ta tadosa amma sai tadake tace ,aaa bana son akore su,kawai dai yamanto bani aiki da kayan su,,,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [5/5, 9:14 PM] ‪+234 703 055 6607‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣4⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI Shakuwa maikarfi ya shiga tsakanin Yusuf da maryam, Har takai koda yaushe suna manne da jikin juna su, Tundai maryam din wace ke ta aikin zuba shagwaba don duk Yusuf din ya rude a kan ta,. Saidai har zuwa yanzu babu shiri sam tsakanin maryam da maman Choima, Amma duk wanan kiyayyan da grandma take gwadawa maryam , Maryam dun sam bata nuna damuwan ta akai don , A mma acikin ran ta abin na damun ta sosai saboda dai da mijin tane take daurewa, Watan maryam uku ke nan yanzu a Abuja tare da auren Yusuf,, Maryam din ta murje abinta,don tasawa kanta kwanciyar hankali, Duk zaman da Maryam tayi a,gidan Yusuf bata taba rokon shi komai ba,dai,dai da abin abincin da take amfani dashi, bata cewa akawo, sai dai tayi amfani da,abin da ta gani kawai, Duk wanan abin Yusuf din yana hankalce da maryam, Sai mamaki kawai take bashi saboda irin hakkurin ta dakuma juriyan ta, Takardun fitan su waje yafito inda yadawo dasu daga office, Maryam bata kusa yau ko da ya dawo tana can kitchen tana aikin, Sai bayan ta gama hada komai ne ta samay shi a cikin falon shi na sama Saye take da riga ruwan silba mai dogon hannu,an matse tsakiyan , A lokacin yana tsaye yana hada wasu na,urorin wuta, shigowan ta falon da sallaman ta yasa shi saurin dago kai, Da yar murmushi makale a fuskan shi, ido ya tsura mata har zuwa lokacin da ta karaso gurin nashi, Ajiyan zuciya ya saukar daidai lokacin da ta karaso gurin nashi, Ina kika shige tun dazun maryam, nadiba dakin ki bakya cikki, Kitchen tace mai a takaice, mikewa yayi tsaye yakara inda take, Hannuta ya riko ya rike a cikin nashi yana cewa, That's why na hana wanan shiga kitchen din don kada a shiga min time dina, Yakarashe zancen da lakutar mata hancin kara jawo ta yayi Inda a tare suka fada saman kujera guda yana rungumay da ita a jikin shi, May kika dafa mun yau ya tambaye ta cikin matse mata yan yatsun hannun ta, Cikin girmamawa tace sakwara na yi don grandmother, Yaji dadin wanan maganan data fadi saboda ya na hankalce da ita akan irin kulawan da takeyi ma ta, Zai yi magana ke nan sukaji motsi turo kofan falo da karfi saida ta iso tace excuse,. Kokarin mikewa maryam keyi amma sai taji Yusuf din ya kara matse ta a jikin shi Muryan shi taji cikin wani irin tsawa yace Get out, A gigice ta juya baya jikin ta na rawa tan dan rusun nawa tana cewa sorry sir, Maryam din ya daga a jikin shi inda ya mike rai bace ya bi bayan ta cikin masifa, Da sauri maryam ta riko hannun shi nan yaja guri guda ya tsaya cak, Juyowa ya yi da idon shi da suka canza a lokaci guda, Amma kuma sai ya kasa cewa maryam din komai, Shiru ne yadan ratsa falon a lokacin maryam ce tai saurin kauda shirun, Tace uncle don Allah ka kyale ta don ba laifinta bane kila da abinda ya kawo ta, Muryan shi narawa yace maryam don may mai,aiki zata shigo min har nan bayan tasan cewa dokane agida, Koda baki nan sam banyarda da mai aiki ta shigo part dina ba tun lokacin danagani littafi, Zanyi maganin ta don gidan zata bari gaba daya, Ranshi a bace ya dauki remote din dake gefen shi yana dannawa yace ita dabbace dazata shigo muna daki babu sallama, Uncle don Allah kayi hakkuri don dai ni iya zamana agidan nan ban taba ganin sun hau saman nan ba, Dole a kwa dalilin zuwan ta nan din dan ko ba halinsu bane, Bai, yi magana ba sai idon da ya zuba mata kamar mai nazarin zancen ta, Sai a lokaci ya duko passports guda biyu ya mika mata, Sai da tadan juya ta duba cikkin mamaki sanan ta bude Passports ne na fita kasan waje tare da Visa, kai maryam tadago tana mai kallon mamaki, A lokacin ya koma yazube kan kujerar da ke kusa da wanda take zaune, Wata irin ajiyan zuciya ya sauke sanan ya furzar da iska daga bakin shi, Har zuwa lokacin fuskan shi da sauran fushi a cikin sa, Kwantawa yayi da bayan shi saman kujera yadan lumshe idon shi, yace, Am hungry maryam, Kallon shi tayi cikin yaudar so tace yau da wuri zakaci abinci haka ? A cike da kasala a muryan shi yace sakwara fa kikai muna yau, Cikin murmushi tace ai yana dinning yana jiran ka dama, Mikewa yayi da sauri yace good Sai ki tashi muje ki bani kafin miyauna ya tsinke ba mussu maryam din tamike tabi bayan shi, Zuciyar ta fam da mamakin Yusuf yadda ya sake jiki da ita haka suke morewa Yusuf wanda zai kai awa daya aguri batare yai magana ko guda ba, Tun daga saman steps suka fara jin kamshin girkin a falon , Sundan kara steps ne suka hango yar tsohuwar zaune saman kujeran dining din ale,ale tana kwasan gara abinta, Tun basu kara saukowa ba,suka ji muryan maman Choima tana cewa, Cikin yaren su da fada na aika akiraka,kazo muci abinci amma shine don kana tare da,wanan muguwar yarinya ka koro yar aiken nawa, Da sauri ya kalli maryam don maganar ta ya zama gaskiya ke nan, Da kai maryam ta nuna mai dacewa su karasa mana, Abincin da yagani a saman dining din shi ya karasa shi kaguwa da ya zauna, ya fara ci, Don rabon shi da abinci tun abinda ta bashi da safe ya karya, Maryam ta gaida mama tare da zuwa kusa don ta zuba ma Yusuf din, Amma sai maman Choima tace cikin bacin kada maryam ta taba mai abincin da zai ci tabari ya zuba da kan shi, Dariya maganar taso ta ba maryam din don dai tasan cewa itace tai aikin da hannun ta ai, Don may za,ace wai yanzu kada ta taba wai ko don kada tasamai cuta, Juyawa maryam din tayi daniyar barin gurin, ji tayi an riko mata hannu, Ko bata juyaba tasan cewa Yusuf ne ya riko mata hannun nata, Cikin yar sakin fuska maryam din tace uncle zan je in hada ma ruwan tea ne, Ganin cewa ba bacin rai a fuskan nata yasa shi saketa, zuwa kitchen din, Sam maryam batasan cewa Yusuf yana bayan taba kitchen din kusan a tare suka shiga, Hawaye take gogewa a hankali da bayan hannun ta batai aune ba sai ji tayi ya riko mata hannun, Cikin yar razana ta juya da sauri ganin Yusuf ne tai saurin wayancewa da cewa uncle bakaci abincin bane, Baiyi magana ba sai hannun shi da yakai a fuskanta ya kara goge mata fuskan ta , Sannan ya dan jawo tazuwa gaban zinc din yasa ta gaban shi yai kaman ya kwanto mata, Cikin murya mai kama da rada yace kada ki kuka pls na san cewa grandma bata kyauta maki, Cikin daga hannu maryam tace haba uncle ai nima grand ma dina ce tunda takace don haka banga abinda zatai min yasani bacin rai ba, Ni ina dai tunanen gidane kawai,ido ya kura mata har zuwa wani lokaci sai ya sake mata hannun,, Yusuf bai koma dining din bs falon shi ya wuce abin shi zuciyar shi a cunkushe da bacin rai Ranan karfe takwas sun shige master bed room shi da maryam wace ganin baici abinci ba tadan mai simply noodle takai mai har part din shi, Haka rayuwan su taci gaba da tafiya inda maman choima taci gaba da tsangwamawa maryam Ita ko maryam tana kokarin kauda kanta gare tana kaucewa damuwan mijin ta, Satin da ya kewayo ne tafiyan su yazu don haka suka shirya tafiyan su , Inda maryam ta nunawa uncle cewa ya kamata su je da Pipkin, Amma fir uncle din yaki sai cewa yayi wanan tafiyan nadaban sai in za suyi wani komawa zasu tafi dashi, A waya takira Anty n ta dije tana sheda mata zancen tafiyan dije taimata yan nasihohi ta kuma bata wasu yan dabarun zanan aure again, Haka ma safiya ta dauki lokaci tabawa maryam yan shawar wari , Kasar Italy suka fara sauka inda Yusuf din zai tsaya don wasu harkokin business din shi, Don haka bai samu wani enough time din zama da yar amaryan tashi ba so sai, Wanan shiga da ficen da Yusuf yake faman yi a kasar Italy din ya jawo mai gagarumin nasaran samun cigaban ckamfunan shi sosai don sun samu nasar sa hannun jari a,wasu kamfunar kasar, Ana gobe zasu bar kasar Italy din ne yadawo gida agajiye saboda aikin da suka sha guraren sa hannu, Rungumay yake da coth din shi a hannu sai hannayen shi da yazube su cikin aljihunshi, Wanka ya fada inda yafito yasamu maryam din cikin wani dogon riga mai hula, Abinci tagabatar mai sai yadan tsankwara kadan yace ya koshi don shi yanzu girki inba na maryam bane sai dai yaci kawai, Kokarin lalabanta yakeyi a lokacin amma sai maryam din tana kokarin zulewa, Tsayawa yayi da mamaki yana kallon ta sai ce mai tayi ai ya kamata ya huta don taga yagaji ne yau Cikin mamaki yace maryam karda ace kina nufin bazaki iya daukan dawainiya naba, No no no kada kizamo min haka pls ban da ra,ayin yin mata biyu kin wadace a rayuwata maryam kidaure da duk wani bukatana, pls, Indan har kin min haka kin min komai pls kin mai dani dan gata ke nan, Murmushi maryam din tayi tace cikin yar dariya baka da matsala anan uncle, Yaji dadin maganar ta don haka yace idan har haka gaskiyane ina son yau atabbatar min da honey moon nazo, Dariya tayi don ta gane wayon manya yake son yai mata kawai , Yau kan ba honey moon tana batun gudu yajawo ta zuwa jikin shi yana dariya Nan ya nemo bakinta ya manne da nashi a guri daya Can wata duniyar suka lula aciki irin duniyar da baka gane haske da duhu, Daga italy suka wuce kasar Hong Kong nan ma dai sun morewa rayuwar su kamar ba gobe, kuma, Wanan tafiya yasa maryam kara shiga farin ciki wanda yamantar da ita duk wani shakku da damuwa, Saura kwana biyu subar kasan maryam ta, tashi da zazzabi amma kuma baidauki lokaciba tasamu sauki, Amma duk da haka saida Yusuf yakaita asibiti don adiba lafiyan ta sun gane gajiyane kawai yadan damay ta, Sun jima sosai a Hong Kong din don maryam ta watsake sosai kafin subar kasar, Yusuf cikin wanan tafiyan ne yai ma maryam set, din funitures ga gidajen shi uku na kwantagora Abuja sai Lagos, Batare da sanin maryam din ba ya turo su gida Nigeria ya sa agyara mata ko ina, Gurin Sonny yake kokarin zuwa da ita don su dan ganshi amma bazasu dade ba acan don zasu wuce Dubai ne daga can, Maryam ta zama babban mace ta goge takara wani kyau da haske ga hips da ya wani baje mata abaya, Kiran ta na "ya mace ya fito tsab ta zama classic lady, yanzu don ko ina zata iya shiga don takai, Sai dai daga maryam har Yusuf din su na jin dar din zuwa gurin Sonny din, Amma kuma Yusuf yana da bukatan zuwa kasan don haka dole su tafi garin, ZEEE MAKAWA YELWA, [5/5, 10:20 PM] ‪+234 703 055 6607‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣5⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI JAMA,ATUL MUSLIMI RAMADAN MUBARAK 👏👏👏👏👏👏👏 Sun bar kasan Hong Kong cikin jin dadi da,walwala, Ga wani irun mugun shakuwa da yashiga tsakanin, Don kowa naji da dan uwar shi sosai,, Idan Yusuf yana gida tilas maryam tana manne a jikin shi idan kuma yana office ne ko wurin wani business to waya ne akai,akai a tsakanin su, Hakan yasa farin cikkin su kullun yana karuwa ne akoda yaushe godiya sukewa Allah, Matsalan maryam yanzu guda ne shine yan uwan Yusuf da suka sasu a gaba, Duk da ba yaren IBO maryam ke ji ba tana fahintar wasu abu a wasu lokutan, Saboda basu iya magana cif da yare zalla sai sun jefa English a ciki musan man ma shi dan gogan nata, Sun sauka South Korea amma sai Yusuf bai sauka a gidan Sonny ba, A hotel mai kyau da tsada suka,sauka shi da black beauty din shi, Tun shiga shi kasan yake sa ido ga yar amaryan shi wace a yanzu tazama mai wani wani sashi na rayuwar shi, Saida ya dan huta kwana biyu sannan ya nemi Sonny din, Sun yi murna sosai da ganin junar su a wanan lokacin Duk da Sonny yasan cewa Yusuf bai shangiya amma sai da yai mai tayi shi, Wani irin harar ya watsa mai tare da daure fuska Yusuf yace kokai ina fatan ka bar wanan akidar very soon Dariya yadan yi mai kama da yake yadan ka da kan shi alamar da wuya hakan, Kurba guda ya shanye cup guda ya kara zuba wani ya aje a gaban shi, Zagayowa Sonny din yayi zuwa gaban Yusuf inda ya hau saman table ya zauna gab da Yusuf din, Yusuf hankalin shi na ga wani takarda da yake duba na,wani harkan business wanda zai iya kawo gida Nigeria har a samu karuwa, Muryan Sonny ce ta katse yana tambayar shi labarin garin da Sonny ya kai shi, a Nigeria, Murmushi Yusuf yadan yi yace suma suna kewan shi ai, Ina wanan Baby din nawa take yanzu ne ? Tambayar ta tsayawa Yusuf cak amma ba wani shayi ko wani dari yace mai ta na nan, Da sauri Sonny din ya dan waiga kamar wanda zai iya ganin maryam din a lokacin, Sai kuma yakai wa Yusuf dan duka acikin yaren su na IBO yace kafaye tsokana Yusuf, Yusuf a cikin daure fuska ya ce, ba wasa aciki tare muke yanzu haka da ita, We haven married six months ago, What's cikin daga murya Sonny din ke tambaya, "Yes, of course" Yusuf ya bashi ansa da hakan, Cikin mamaki Sonny din yace yanzu kayi aure Man shi banda ko labari ban jiba ko ga,wani, Takardan dake hannun shi ya dire saman table din yace, You now how my sweet religion is, Basai munyi wani bidi,a ba zamu iya yin auren mu a cikin mutunci bukata kawai shedu su sheda hakan, Hannun shi ya tafa raf raf raf sau uku ya ce congratulations, Sai ya duko kan shi gab da kunnen Yusuf din ya ce, You are the most lucky man , I ever meet in the world, Maganar Sonny taba wa Yusuf mamaki sosai Sonny din ya ce gaskiya nai maka murnan samun wanan yariyar a rayuwan ka, Duk da dai kai ba,wai kadamu da mata bane balle kasan irin abin da na hango ga wanan yarinyar, Amma yanzu tun da ta na gurin ka ,a sannu zaka gane ko waye ita, Nagode kawai Yusuf din ya furta cikin kaguwa irin yadda abokin nashi ke santin matar shi a gaban shi haka, Yusuf ne kau da hiran matar tashi daga bakin Sonny, Harkar business suke tataunawa akai ta yadda abubuwa za su zo mai da sauki, Sun dauki dogon lokaci a office din Yusuf din suna tataunawa akai, Sai lokacin da Yusuf zai wuce ne Sonny yake tambayar shi inda maryam take don yazo su gaisa Tare da cewa shi a matsayin shi na babban aminin shi zai hadawa Yusuf da maryam yar party na aure don duniya ta sheda, Mamata boye ta nakeyi don bani son maza yan duniya masu halin dan akuya su sa mata ido, Hararan shi Sonny din yayi yace kada ka dauke ni haka inda dai baka aure ta da duk yadda zan rabaka da ita zan yi don in more mata, Kaji mara mutunci inji Yusuf ya harari Sonny din yace ya kamata ace kadaina wanan irin akidar ka samu family hakana pls,, Murmushi Sonny yayi tare da bubuga kafadar Yusuf din,, yadan girgiza kan shi, Sai da yaba da baya ya ce zan di ba acikin addini ko zan samu wace tai daidai dani, Saboda a gaskiya bazan iya shiga addinin ku ba don naga kuna da tsananin bauta har sau nawa kuke bauta in a day, Abinda Yusuf yariga yasani ne dama Sonny bazai taba musulun ta, Koda yaso musuluntar aminin nashi ne don yasan idan ya auri maryam zata kokarta a kan shi, don yayi addini, Sai yazu yake godewa Allah na rashin cutawa yar mutane da bai yi ba dakuma cutawa rayuwan shi kan shi, Don dai Sonny bazai iya musulunci ba gashi ya kasa tsayi a Christianity balle musulunci mai akidoji, Har hotel din da suka sauka Sonny yakai Yusuf sai dai bai shiga ba don adan buge yake alokacin, Amma yai alkawarin zai kawo ma su ziyara zuwa gobe indan ya fito, Washe gari ganin da Sonny yaiwa maryam din sai da ya tsorata sosai, Don maryam din ga kyau, ga iya dressing ga zubi daganin ta ka ga matar manya ce, Fatan jikin ta yai mata wani lub lub, tankar irin mantan Pakistan din na dakr cikin daula, Ga natsuwa da kamala don komai nata a natse takeyin shi ba garaje, Wanda hakan ke wani kara mata aji da class, a idon mai kallon ta,, Sonny yai masu murnan auren da sukayi inda ya ba maryam din kyautan wani dan kit da kuma wani dan karami box, Duk kan su sun san cewa kyautan Sonny ta bajinta ce a ko da yaushe, Basu kara wasu kwanaki ba masu yawa suka bar kasan zuwa kasar Dubai, A can zai ga wasu mutanen da yake bukatan ganin su don su karfafa har kan median a Africa, A kasar Dubai maryam tai mamakin ganin yan Nigeria a can birjit, kamar a kasan su, Wanda duk harkokin business ne yakai su kasar, Gashi kusan kowa da matar shi zaka gan shi a gurin wasu kuma matan banzane kawai anje shakatawa, ne kawai, A gidan wani cin abincine suka hadu da wani matashi dan Nigeria wanda yaje harkan business sai dai bawai ya saba bane, Shida kanshi mutumin mai suna Suleiman yai wa Yusuf magana, Anan hira ta balle a tsakanin su inda Suleiman ke ba Yusuf labarin cewa ya shigo ne don yadan fara taba international business , Shi mutum Minna ne Niger state yana aiki kuma yana son harkan business, A nan Yusuf yadinga bawa Suleiman shawarwari akan business Daga karshe sukayi sharing din nomban su wa junan su, A wani dare ne Yusuf yai waya da KB inda KB ke sheda ma Yusuf wai Jibrin yai aure Aure fa inji Yusuf wanda yai tambaya a cikin mamaki ? KB wanda, yaba Yusuf din ansa cikin dan rudewa ya ce, kwarai kuwa, Auren ne ba dole sai kasani ba inji KB din don wace ya aura din, Ba safiya bace ya aura sai a lokacin maryam wace take bayan shi kwance rub da ciki tai magana, Cikin dan dagowa da ga kwanciyar da take yi ne tace wace baka zata ba dai ya aura, KB kuma a lokacin ne yake ce mai ai Jibrin Sadiya ce ya aura, Boye mamakin shi ya yi da cewa masha Allah nai mashi murnan samun wanan karuwan, Amma shine bai fada min ba sai dai kawai inji bayan bukin, KB yace sai dai in Allah ya dawo muna dakai lafiya zaka ji ai , Bayan sunyi sallama ne Yusuf ya turawa Jibrin da text din taya shi murnanan aure, Azaton shi zai turo mai da ansa amma sai ya ji shiru ba replay Sai daga baya ne yake tambayan maryam ko tasan dalilin hakan, Maryam wace take a zaune a gaban mirrow tana daura dan kwali tace Ai Safiya ta mahuta wallahi maganar sai ta ba yusuf mamaki, Maryam nasan cewa kinsan wani abu acikin wanan maganar amma baki fada min ba, Maimakon tai mai bayani abinda ke faruwa sai ta share da cewa uncle je kai wanka kada bakin mu su samay ka bashiri, Ya fahinci batason yasan wani abu akai don haka yabar zancen kawai, Baki sukayi wani mutum dan Nigeria da ke son su hada wanan business din da zasu hada a Dubai din, Sun sa ranan meeting don haka sun dauki lokaci mai tsawo suna wanan plan din, Matar chairman din comety din nasu ita takawo shawaran cewa su ma matan su ya kamata su kawo nasu gudun mawan, Wanan taron da matan suka sa zasu ya jawo wa duk wata mace dake cikin gungiyar samun cigaba sosai, Kafin lokacin Yusuf wanda yasan cewa matar yarinya ce ba wai ta,waye bane kuma sauran matan sun mahaife ta Wani dan training school na mata ya kaita, cikin kwana uku maryam tazama wata irin gogagan mace yar bariki, Ranan taron nasu maryam tare da matar da tai mata training din itace da kanta ta,shirya maryam din, Daga ciki kwalliya irin ta matan hausawa tayi zani da atamfane jikin ta, wanda yasha dinki irin na Dubai design Daga,sama ta dora wani irin alkyabba irin mai tsadar gaske din nan, Daga nisa kasan cewa sai matan manya ko matan manyan sai wace ta isa, Hular alkyaban yadan rufe mata ko ina daga kan ta, Zakace ko mayafine ta yafa akanta alokacin don irin yadda yai mat, Hannun ta an jera zobbunan gold sun cika mata yatsu, Wuyan ta na saye da gold kiran Dubai ya na daukan ido don tun daga nesa zaka hango shi, Takalmin kafan ta da yar jakar hannun da ta rika shima abin kallo ne, Ga wani asirttacen kamshi dake tashi daga jikin ta, Shi kan shi Yusuf din sai yaga maryam din tashi ta canza mai tankar ba ita bace a gaban shi yau, Yusuf bai san sanda ya jawo maryam din zuwa jikin shi ba, Jikin shi narawa ya na kokarin kai bakin shi cikin nata, Sam ya manta da zancen matar da ke tsaye a gefe tana jiran sallama, Wayan shi yabawa matar yace tai masu photuna, Ganin irin yadda ya rude baiko iya boyewa agaban mutane maryam din tace haba uncle Yace gaskiya maryam wanan matar zata hada min duk wasu abinda nake bukata a lefen ki, Haba wani lefe kuma duk wanan sayayyan da nasha ni sun isheni Alhamdullahi ko hakan, Ya maryam tsadar shigar ki ko a yaushe shi mutunci na a idon duniya don za,a san ban tauye maki hakkin ki ba ta ko ina, Maryam tai dariya tace aiko a haka Alhamdulla don an san baka tauye ni ba A, a maryam nafison ansan cewa ke din ta daban ce zai fi min ni mutum ne mai son ko yaushe inga matana acikin kwalliya, Irin yadda maryam tashigo dakin taron ya tayar wa sauran matan da hankali sosai Don gashi dai itace karama daga cikjn su duk sun haifeta wasu kuma sun girmay ta, Amma sai gashi ta tsone masu ido shi da kan shi Yusuf yai mata rakiya agurin yana nan nan da yar matar nashi, Duk gurin suka bisu da kallo sai da yaga gurin da ta zauna yadan duka yai mata magana a kunne wanda yasa maryam din sake dan murmushi da ya kara mata kyau, Kishin haka yarufe wasu mata daga ciki da suke ganin cewa su wata tsiya ce da farko,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [5/5, 10:21 PM] ‪+234 703 055 6607‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣6⃣ Cikin jin dafin samun nasarorin da Yusuf yayi suka dawo gida Nigeria, A cikin nasarorin da yasa mu harda zama shugaban youth na median na Africa, Sun samu kowa lafiya agidan inda suka,samu taro mai kyau, Maman Choima kallo guda taiwa maryam ta kauda kai agare ta saboda irin yadda taga canji cikin lokaci guda, Pipkin yafi kowa murnan ganin little mum ta dawo a lokacin, Tunda Yusuf suka sauko ya shiga gida bai fita ko ina ba don yana son hutawa, Maryam taiwa duk wani wanda ke gidan atare da,su kyauta ta musan man, Hakan ya sa masu son matar ogan nasu azuciyar don dai sun fahinci bata da keta,,,,,, Lokacin sanyi ne, don haka kusan goma na safe amma Yusuf ya na kwance makale da matar shi wace bata da wani hutu idan yana gida, Barci sukeyi amma ajikin shi take kwance saboda jikin su akwai gajiya, Wayan Yusuf wace ke yashe a gefe guda tai kara har wayan ya kusa karewa suna kwasan barcin su a lokacin, Maryam ce tai kokarin dagowa daga saman kirjin Yusuf, din, Itace tadan dauko wayan daga inda yake a yashe, Idon shi da dan sauran barci a kai sai kuma haushin wanda ya tada shi daga barcin shi da yake yi na safe mai dadi Samuel ne ya gani a rubuce saman screen din wayan shi, Samuel how are you ? Brother we are coming to Abuja this morning with papa, Yusuf din wanda yaji maganar kamar daga sama zubur ya mike daga inda yake kwance, Maryam wace a lokacin tana cikin bathroom shi kadai yai zaune a bakin gado yana tunane da nazari, Shawara guda shine ya kai su gidan shi guda kawai ya kai masu masu aiki can, Ganin shi a bakin gado cikin yanayin damuwa ya sa maryam saurin karasowa gurin shi da,sauri tana cewa uncle lafiya, Kan shi yadaga a hankali ya kalle ta kamar kada ya fada mata sai yaga ai sani zatayi, A hankali kamar wanda zai fadi wani mugun zance rai a dan bace Hakan yasa maryam wurgat da dan towel din dake a hannun ta kasa, Da sauri takaraso gu4in shikin tambaya take cewa May yafaru ne wai batare da ya kalle ta ba yace wai baba da yan uwana zasu yau din na, Maimakon maryan ta nuna razanan ta afili sai Yusuf yaga tana murmushi, Tace ashe barin fita in fara abin taron baki yau muna da bakine haka agidan, Kallo yabita dashi na mamaki don yazaci ta nuna mai kyamar ta karar akan su Ta mike da niyar ta wuce taji ya riko hannun ta, ta baya cak ta tsaya guri guda Muryan Yusuf ne da yajawo ta zuwa jikin shi yana cewa maryam baki tsoron zuwan su gidan nan, Tsoro ta tambaya cikin mamakin jin maganar shi tana mai wani irin kallo A kwai matsalane halan, gazuwan su tatambaya cikin nuna rashin damuwa, Bai ce komai ba shima mikewa yayi batare cewa komai ba, Sai sai maryam tai masu girki inda takuma sa a,gyara masu dakunan kwana, amma Yusuf bai da labarin haka,, Sun iso garin bayan sallan la,asar alokacin maryam tana dakin ta na sallah, Azaton Yusuf sukadai ne zasu zo yan gidan su sai gashi ya ga mutane masu yawa, Yan manyan church din su ne tare da mahaifin shi wai sun zo wani taro ne a wani church irin nasu, Duk yawan abincin nan sun cinye abinsu sai kari suke bida, Nan ihu yatashi da kiran sunan Jesus, maryam tun daga dakin ta na sama take jin wanan ihun nasu, Sai kalman Innalillahi take iya maimaitawa kawai, a bakin ta, Yusuf wanda yaso yakai su masauki amma fafir sukace su a an zasu sauka, Sau guda maryam din ta sauko kasa gaida su suna zaune ga kwala be a gaban su sai dai bazata iya tantance kona maye ba, Cikin zulunbun Hijab din ta har kasa baka ganin komai nata sai dan round face din ta kawai, A natse take tafe Yusuf na gaba tana bin shi baya cikin natsuwa, Duk kunya takama shi ganin irin yadda suka baje tumbi da kuma sake jiki suna ta faman dura giya a cikkin, Duk kunya da nauyi ya kama Yusuf wanda rayuwan shi duk yabaci amma bai,da yadda zai yi ne kawai, Kowa sai kallon maryam din yakeyi kamar zasu cinye ta danya, Tundaga wanan ranan maryam batakara saukowa ba, Saidai Yusuf yasayo mata abinda za ta ci ko take bukata, Kwanan su goma sanan sukabar masu gida inda kafin su wuce baban Yusuf yake cewa shi yafi son Yusuf ya auro yar yaren su, Tafiyan su ba karamin dadi yaiwa Yusuf ba wanda ya dinga ji tankar yai kuka saboda ansha mai giya a gida, Masu gyaran gida yaturo sukai wa gidan nashi, kwal komai saida aka wanke, Yafara zuwa office bayan dawowan su a can KB yasamu Yusuf yana bashi labarin yadda Jibrin ya auri Sadiya, A cewan KB wai harda mahaifin shi yace kada ya yi wanan auren amma Jibrin din ya dage akan sai yayi,, Kuma yanzu ga shi sai sukan Yusuf da maryam yake yi duk inda ya zauna, Yusuf yaso ya bata rayuwan shi akan yadda Jibrin din yai mai sai dai yaga cewa babu abinda a gwada mai a rayuwa yanzu, Baiwa maryam zancen ba sai bayan kwana biyu a lokacin yana aiki a cikin computer shi Maryam tana zaune a kasa ta sa fruit a plate sai sha takeyi Idan ta sha tabare ta sawa Yusuf a baki yana yi yana aikin shi,, Maryam Yusuf ya kirata batare da yadago kan shi daga aikin da yakeyi ba, May kika sani akan rabuwan Jibrin da safiya ? Tambayar ya bata mamaki sosai a lokacin don bata zaci zai kara maganar ba, Uncle gaskiya ni abinda safiya tafada min bawai nayarda bane, Fada min may ta fada maki maryam bata boyewa mijin nata komai ba azancen da safiya ta fada mata, Hmmmm kawai yace bayan da ya fahinci maryam tagama zancen ta, Maganar tasa Yusuf ya kasa aikin dake a gaban shi yadan dago daga duken dayake, Hannayen shi ya hada guri guda yadan fura iska ta tsakiyan su,,,, Dasafe idan Yusuf yafita gurin aiki sai shida yake dawowa gida wata rana yakan dawo daguri kuma, Yau ma sun rabu lafiya tsakanin su Yusuf yatafi yabar maryam tana daga mai hannu Ta koma ciki ba a dauki wani lokaci ba barci ya kwashe ta, Kaman ance ta bude idon ta sai wata budurwa tagani a dakin, Ta na saye da dan guntun buje daidai cinyar ta, sai rigar jikin ta baki mai kama da shimi, Tashi maryam tayi taga kwancen da take cikin mamaki don budurwan ta gaban mirrow tana shafa jan baki a bakin ta, Cikin hausa mai surki da yare tace kin tashi matan yayan mu, Murmushi maryam tasake mata, nashigo kina barci shine nace barin kyale ki, Har nai wanka baki farka ba sai yanzu dama zan fitane akwai saurayi da zai zo, Zaune maryam takai inda ta sako kafafun ta kasa cikin mamaki, Amma ga yadda taga budurwan na murmushi sai tadan sake ranta itama, Yanzu dai mu gaisa sunana Ruth ni kaunan mijim kine da fatan ya baki labarina, Takarashe zan cen da son jin ansan da maryam zata bayar Cikin murmushi maryam tace kece Ruth ashe ko yau she yana zance a kanki kuwa Ruth taji dadin hakan don sai da ta dan yi murmushi mai baiyyana hakora, Maryam tace barin kawo maki abinci ko kafin ki fita, Cikin daga hannun ta tace da sauri No, no no ki barshi kawai Sai nadawo idan brother ya dawo saiki fada mashi pls, Daga haka tafita kusan a tsirara take maryam ta sauke ajiyan zuciya bayan fitan ta, Hamdallah ta yi ga ubangiji da yayo ta musulma, Abinda maryam ta lura dashi shine Yusuf naji da sister shi Ruth sosai don haka tadauki alwashin kyautawa Ruth din itama, Duk yadda yake son kasan cewa da Maryam din kamar da yanzu bai samun haka, Tun yana daurewa har yakai yau bayan yadan shawo kanta ne komai ya kammala, Sai kawai yaga har barci ya kwashe ta ko yanzu sam bata son bashi hadin kai kamar farko, Saman dining table suke kowa na kokarin karyawa amma banda maryam wace tasa ruwan tea din ta gaba tana kallo Yusuf ne da kanshi ya matsa mata har tadan sha rabi, Abuguda ke damun maryam yanzu kamar yadda su Ruth da Grandma ke damun su da waka tun da asuba ko tana son yin addu,oi basu bari saboda ihu da kuma suraitan su, Yau ma kamar kullun bata samu barcin dare da dadi ba takai wani lokaci a kwance, saboda masu wakan church dake tashi cikin dare suyi tayi, Wanka maryam din tafito tana zaune gaban mirrow Yusuf yashigo dakin yana kokarin daura cliffs a hannun rigan shi, Tun daga nesa tace mai ina kwana uncle ya ki ki beauty, nashigo na samay ki kina ta barci ai, Murmushi maryam tayi tace yanzu sai da safe nake dan samun barcin don hayaniyan nan na dare bai bari inyi barci, Baiyi magana ba sai ido da yadan tsura mata tausayi tabashi acikin rashi don yasan cewa dama hakkuri takeyi kawai, Don irin yadda suke yi da wata ce yasan da yanzu an kwashi yan kallon dan abin nasu harda gaiyya aciki, Sallama yai mata yace zai dan shiga gari don ba aiki a ranan, Bayan fitan shi tadan sha fruit don shi abincin ta ita saboda ko da bata damu da abinci ba ita, Saida taga tadan kara kwantawa don ji tayi still barcin bai isheta ba , Anty ce tafado mata arai don shi baba yace ya yafe mata tadaina kiranshi idan yaso shida kanshi zaiwa mijin ta magana abata waya, Anty ta,dauki wayan cikin wani murya wanda maryam din bawai tasan ta dashi bane, Gaisawa sukayi sama sama batare da tasakewa maryam din ba, Sai maryam dince ke cewa abata su Assalam su gaisa, Bayan sun gama wayan ne sai tunanen yadda yanzu yarta ke mata yadamay ta, Daga gurin ta koma barci abin ta har akai sallah azuhur maryam bata farka ba, Yusuf yadawo daga massalaci yaganta a kwance shi da kanshi yata da ita, Ido ya tsura mata kamar mai son ya gane wani abu acikin ta, Maryam ya kira sunan ta inda ita Maryam din ta ansa mai a hankali, YUSUF yace wai mai ke samun kine haka naga duk yanzu kin koma wata iri jiki babu kwari, Sai barci all the time, may yasa hakane wai, ? Maryam tadan langabe kan ta tace nima ban sani ba uncle haka kawai nake jin ba dadi ko da yaushe, Gaskiya anjima zakai ki kiga likita don yadiba min ke ko baki da lafiya ne, Tana kokarin mikewa,zaune ne tace to aini lafiya na kalau uncle, Gaskiya ban yarda ba inji uncle yace wa maryam din, Dole ne aduba minke don duk kwanan nan an hana min, samun wanan ni,imar da aka saba bani Din yanzu kusan manaji kawai nakeyi ban samu ina kashe kishin sha,awata kamar da,, Kunya ya kama maryam din wace ta boye fuskan ta cikin filin dake kusa da ita, Kwana biyu maryam taki yarda,su je gurin likata ta dage wai ita lafiyan ta kalau gajiyan tafiyan jirgine ke tambayar ta, Shiko Yusuf ya kasa barin ta ta huta kullun sai kokarin diban rabon shi yake yi gare ta, Hakan yasa jikita yai weak sosai har saida takai kwance, Bashiri dole suka tafi asibiti don adibata, saboda yadda take jin jikin ta, Awon farko likita yagane cewa cikine a jikin maryam na wata uku, Gashi kuma saboda rashin samun hutu har cikin shima yana son samun problem, Yusuf tun agaban doctor ya rungumay maryam cikin hamdala ga ubangijin shi Mutum na farko da Yusuf din ya fara kira itace Ànty Dije tanuwa Yusuf din farincikin ta sosai a fili, Amma sai dai abinda ya kula dashi bata tambayi lafiyan maryam din ba, Amma kuma sai bai dauki zancen da muhinmanci ba, Ita ko maryam safiya ce takira ta sheda mata duk yadda,sukayi da likita da bed rest din da aka bata, Anan sadiya tai wa maryam alkawarin zuwa ta diba ta, Saboda sanin irin mutanen da maryam din kezaune da su, Mahaifiyan safiya bata da matsala indai har al,amari na maryam ne, Aikuwa washe gari safiya tafara shirin tafiya,Abuja inda tayowa maryam din tsaraban kanyan miyan hausawa na gargajiya, Motar farko tabiyo zuwa Abuja din inda suka iso musalin karfe biyun rana, Maryam taji dadin wanan ziyaran da aminiyar ta takawo mata, Ita ko safiya sai kallon mamaki takewa kawar ta ga kuma irin daulan da Allah yaba ta, Gaskiya Allah miskaraziratin ne, ga bayin shi, Kamar ba maryam wace ke ta aikin wahala agidan yar uwar taba, Gashi duk wahalan nan da tasha don Allah yaba maryam din gurin zama mai kyau gashi kuma Anty tafara kushewa, Yusuf yadawo daga gurin aikin yasa mu maryam tare da,abokiyar ta,suna hiran su gwanin sha,awa, Nan ya zauna tare dasu ya gaisa da Safiya din, inda yake tambayan ta labarin mutanen kwantagora, Yaso ya tambaye ta zancen Jibrin amma sai fasa saboda ko shi bai son ya tuna da maganar , Maryam daga inda take kwace suka hada ido da Yusuf yai mata,wani irin kashe ido Wanda ita kadaice tasan ma,anan wanan kashe idon , Kafadar ta tadaga mai alamar a,a yakara dan langabe kai maryam tai mai da nuni da Safiya wace tabada baya tana kallon TV, Ya juya yana fara tafiya jiki ba kwari yadan juyo yana cewa ai na manta gobe zamu yi baki daga Niger state,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣7⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI YA ALLLAH KA KARAWA ANNABI DARAJJA KA KARAWA MUSULUNCI DARAJA 👏👏👏👏 Tun lokacin da Yusuf ya buga mata waya akan zancen, cikin maryam sai ta,shiga tunane, Shin maganar da Umma da, Yashe suka fada mata akan maryam gaskiya,ne kuwa, To in ma har gaskiyane ai shi Yusuf mai yai mata da har zata hada dashi a cikin maganar, Ita kan ta maryam din har yau bataga wani alaman daga gare ta ba, Don dai duk yadda,take nuna mata cewa tagane may sukayi Bai hanata kusan kullun bugo mata waya ba ta gaishe ta, Uwale ce ta kara kwada sallama Anty dijen zaune a falo, Firgigit Dije tai ajiyan zuciya tadawo daganin ga aminiyar ta uwale, Wani irin tunane kike yi haka Dije ? Uwale ce ke tambayar ta cikin mamaki don son jin ansa, Numfashi ta sauke da nauyi cikin da nuna damuwa a fuskan ta , Tace ke dai Uwale bari kawai wallahi wani magana ne ke damuna, Subbahanallahi inji uwale ijin maganar da sauki dai, Ke ba wani magana bane sai maganan maryam May yasamu maryam din cikin tashin hankali uwale ke tambaya, Bari kedai Uwale wai ashe maryam da kawar ta safiya ni sukaje yiwa asiri kwanaki har tai wanan ciwo din, " Ke, Dije cikin zaro idanu Uwale tace haka nan, Yanzu wani mara tsoron Allah ne ke son hadaki da yar uwan ki, Yarinyar da ba tafita ko ina ko yaushe tana gida abinta, Nima dai shi nagani Uwale, Bayau ba tun da maryam din tai aure da kwana biyu naji maganan wallahi, Uwale Umma mahaifiyana itace tazo tasamay tare da Yashe, wai maryam da kawar ta safiya sun ji gidan wani malami wai ai masu aiki a kaina ita maryam din ta samu miji wanda yafini,ita kuma safiya wai baban yaran nan take so, Innalillahi wa,ina alaihim raji,un, Dije ina ilimin ki da tunanen ki suka tafi dahar ki ka yarda da waman zancen da bai da kai baida gindi, Wanan ma ai zancen shirmay ne koda ace maryam ba yar uwar ki bace ta jini ai zaman da ku kayi yawuce irin wanan cuntan, Amma gaskiya dije baki tunane jiyadda yarinya ta dauke tankar mahaifiyar ta, Anty dije tafadi cikin wani irin murya tace Uwale tunan da nakeyi ke nan ida hakane Maryam tana min hassada ai da baza ta ciga ba da mai dani tankar mahaifiyar ta ba, Ki di fa hatta kayan lefen da wai miji yahado mata daga waje da suka fita saida tace akawo min in yi duk yadda ya dace,, So,sai Uwale,ta kara fahintar da Dijen akan cewa Umma tana son ne kawai ta rabu su da maryam din, Uwale tai mata tuni a kan sunan da zata raka ta gobe a kan wuri, Bayan fitar uwale ne bada wani dadewa ba umma ta shigo gidan, Bayan sun gaisa ne Anty Dije tana mamakin yadda yanzu umma ke yawan zuwa gidan ta, Cikin zanin ta tafito da,wani bakin leda tana kokarin budewa tana leken hanya, Zuviyan Anty dije yasa mata tsoro sosai akan mahaifiyar nata, Wanan dan kwallaban ruwan ciki akeso ya taba jikin maryam din, Wanan garin kuma hayaki zakiyi ki dinga kiran sunan maryam da mijin ta, Kine cewa su rabu har abada, Gaban anty yaba da dammm maganar uwale ne yafado mata arai, Data ce idan maryam bata da alhakin ta duk sherin da taiwa yarinyar zai iya dawowa akanta, Con n rawan murya Anty Dije tace umma, in raba sufa kikace, Umma tace to sai may don kin raba su dije ? Yanzun ke inba rashin wayon ki ba har ace diyar kishiyana wace batakai ko ki diri ba balle ma,ana wai tafiku sa,an daki, Innalillahi umma maryam fa tankar diyar ki take don may zamuyi mata haka ? Dakuwa taiwa diyan nata tace wai ke yaushe zakiyi wayo ne dije, Tun farko sam banso a ce kin dauki wanan yarinya tazauna agurin ki ba, Gashi yanzu sanadin zamanta gidan yasa har wanan yaron ya gan ta ya aura, Da yake ubanku muna fukine shi don yaga gurin ci yadauki yar shi yabayar, Anty, dije taji wani iri a cikin ran ta yadda mahaifiyar ta, da kan ta kewa mahaifin ta wanan mumunar fahinta, Sanan Umma din takara da cewa,kitabbatar da cewa kin yi duk yadda malam yace, To Umma inji Anty dije tadan ja ledan kayan zuwa gefen kujera,, Umma ta mike tsaye tana gyara daurin zanin ta tace tashi ki duba idan kuna da shimkafa ki debo min, Ita dai Anty ta mike tsaye zuwa samo ledan da zata zuba masu, Bayan tafiyan umma Anty dije ta zube a gurin cikin tashi hankali da nadama,,,, Maryam ta gama gyaran jikin ta tadan juya gurin da Safiya take tsaye ta na, gyaran gadon da suka kwanta, Maryam tace Safiya ban san ko may ke faruwa a tsakani na da Anty na ba, ? Murmushi safiya tayi a lokacin da take gyara filon gadon, Abinda Anty Dije da kannen ta suka rufe ido sukai mata yafado mata arai, Idon ta dan runtse ta dan hade wasu miyau takaici dataji sun zo mata, Amma a fili sai ta daure ta furtawa maryam din cewa , Maryam akwai matsala a tsakanin ki da Anty ban,dai fada maki wanan labarin bane, Amma gaskiya an shiga tsakanin ku ke da yar uwan ki, Do min maryam naje gaida Anty bayan ku wuce da kwana biyu, don in kwaso kayana agidan, sai kuma ta ce, "Hmmmm, kawai tace ta girgiza kanta don bazata iya fadin maganar cin fuskan da Anty tafada mata ba, a lokacin, Zaune maryam takai don ta fahinci akwai abinda yafaru a tsakani safiya da yar uwan ta har ita kanta zancen ya shafe ta, ke nan Gaban maryam ya yanke yakara faduwa don tana tsoron ko may za,a ce tafadawa yar uwan nata, da har tai saurin dauka haka,,, Yusuf ya fahinci cewa akwai matsala a tsakanin maryam da yar uwan ta, Anty dije, Amma tunda ba bata fada mai komai ba akai don haka ya share zancen kamar bai san da maganar ba, Sai,dai gaskiya yasan cewa a yadda yasan Anty dije bawai zata iya jure maganar ba,har ta bawa kaunar nata baya ba, haka, Bakaramin dadi Yusuf yaji ba saboda irin yadda yaga Safiya tare da yan aikin su sun hadawa bakin shi abinci, Suleiman ne, ya zo wanan, matashin da Yusuf ya tai maka da shawara a kasan Dubai, Yasamu cigaba sosai ga harkan don har yana shirin komawa kara saro wasu kayan, a karo na biyu, Sanar,ar kayan na electronic bakaramin sana,a bane, wurin samun ci gaba, Tare yazo da wani kawunshi saboda su ma Yusuf godiya taimakom da yai mai, har gida, Sun zowa maryam da tsaraba masu yawa da kuma kyautan turare da agogo wa , maigidan, na ta, Bayan tafiyan su ne maryam da,safiya suka bude kayan suna kallo, suna yaba irin wanan kyautan na bajin ta, A cikin kayan maryam ta dauki atamfa guda da takalman su, tace zatabawa Ruth, ne , sauran kuma gaba daya tabawa Safiya su, Mamaki kwarai ya kama safiya din wanan irin kayan maryam zatace ta bar mata su duka, Maryam ta ce haba Safiya komai ma zan iya maki a duniya saboda irin gudun mawar da ki kai min a duniya, nima, Safiyar kin fa sadaukar da farin cikin ki a kai na kin dauki yan uwana da iyayyena tankar naki, Banda abinda zan ce sai dai in maki fatan alheri yadda kikai min kema Allah yai maki, Ganin zuwan safiya maryam ta dan samu sauki Yusuf yace su shirya ya kai su cikin gari ranan duk sun yi farin ciki da jin zasu fita, Yusuf Yayi hakane ko hakan zai kara sa maryam din ta kara warware, jikin ta, Shiri na alfarma sukayi daga maryam din har safiyan, Duk wanda ya gan su sai sun burge mai shi saboda yadda su ka haska, Wani sabon restaurant da aka bude wanda sai ka isa za a gan ka a gurin, Su uku a table guda suke zaune abincin da ke gaban su suke ci a cikin natsuwa da jan aji, Duk lokacin da Safiya ta debi abinci zata kai ga bakin ta Sai sun hada ido da wanan guy din, dake can gefe guda yana saye da wani glass baki a idon shi, Maryam kan sau guda takai abincin a bakin ta taji bazata iya ci ba, Ga nauyin jama,a ga kuma test din abincin bai mata ba a bakin ta, Yusuf ya hankalta da ita ta kasa cin komai a gurin don haka ya matsa mata akan may zataci a kawo mata, Amma sai maryam din tace ita Fanta kawai zata iya, sha, Dariya abin ya bashi tare da tausayin yar matar nashi, Saboda a duk wanan kayan daulan dake gaban ta bazata ci komai ba daga ciki, wai sai common Fanta,, Da kanshi ya mike zuwa samo mata Fantan sai a lokacin safiya ke fadawa maryam wanan guy din da ya kureta da kallo, a bayan su, Dawo wan Yusuf da zaman shi yai dai,dai da zuwan wanan guy din gurin, su, Kafadan Yusuf din mutumin ya dan dafa ta baya yace, Joseph Emanuel, Yusuf ya juyo don ganin mai maganan, Umar sultan ya gani course mate din shi a Oxford, Umar Sultan Yusuf yace cikin mamaki inda su maryam duk suka bisu da kallo, Sun dan jima rike da hannun junan suna ta zabga hira, Sai daga baya Yusuf ya nuna inda su maryam suke ya na cewa, Meet my wife and her sister Su maryam din duk sun matse fuskan su don kada yaga daman su, a gurin , Da sauri Umar din ya waigo gurin Yusuf ya nuna shi da hannu ya ce, Kana nufin kai musulmi ne yanzu ko? sai ya kuma kasa tambaya, Yusuf ya gane may yake nufi, don haka yace mai insha Allah, Da,sauri Umar din ya jawo Yusuf zuwa jikin shi yana mai ce mai, Alhamdullah congratulation, for be in islam, Nan sukai exchange din noba yace zai ziyarci Yusuf din,,,,,, A hanya maryam ke tambayan Yusuf ko waye umar sultan,? Yusuf yace Umar dan sarautan sokoto ne yana da ilimi sosai na addini dana boko, Suna shekaran karshe wata baturiya diyar wata mai kudi ta lake mai har sukai aure bada sanin iyayen shiba, Hakan ne yasa shi tsaya can yafara aiki akasan amma kungan shi mutum ne mai son addini saidai zaman shi acan ya dan sauya shi kadan, Allah ya kyauta sukace alokaci guda daga haka ba wace takaracewa komai, Gidan bukin ya cika makil da yan suna daga cikki har da uwale da anty dije, Suna can wani daki zaune suna hira da mutane, Wata mace ke tambayar Anty ya labarin su maryam da maigidan ta,? Lafiya suke inji dije nan matar ke bada labarin fadan da tayi da wasu akan auren maryam da Yusuf, Sai wata ke cewa ina mamakin mutane da zasuce wai suna kyamar auren mutum musulmi dan uwan su, Ai da ance yar uguwar yamma zai aura amma wai iyayyenta suka nuna cewa shi furen kan juji ne ba,za su bashi ba, Bashine akace mahaifinku ya fashe mai wanan takaicin ba ya bashi kaunar ki,, Kiran sallah da akayi yasa matan dan watsewa a dakin, Daya daga cikin sune zaune tace idan sun dawo zata tafi, Fitan sauran matan biyu yasa dayan matan da ta tsaya tace yar uwa ashe kece sister din wanan yarinyar da ake hira, Zaki iya tunawa kwanaki ankira ana fada maku cewa an ma yarinyar asiri, Uwale tace kwarai kuwa anyi hakana kuwa, ai matar tace wallahi nice, Nima Sadiya suka shigo gidana suna hira da kauna ta shine naji, A gurin kauna ta na samu nobar sister din naki wai zasu kirata su zage ku, Matar tace hankali duk yatashi a lokacin ina gudun abinda zai samu diyan mutane, Godiya su Anty su kai wa matar tare bata labarin yadda tai fama da ciwon kai, Matar tace bagashi tayi auren cin amana ba wai yaron shi mutumin ta aura don tabashi takaici, shima da asiri ta nemo shi, Gashi tun yanzu ance yasamu kariyan arziki saboda irin shagalin da sukayi da auren, Nan dai taci ga ba da basu labarin akan yadda tasamu kan jibrin yagigice a lokaci guda duk da mahaifin shi yace kada yayi wanan aure amma ido rufe yace sai yayi,,,,,, Musalin karfe biyar na yamma suna zaune a falon su na kasa Maryam ta sayi da wani dogon riga english wear, Ringan yadan fitar mata da dan suran jikin ta don har dan matashin cikin ta yadan fito Yau saboda ta sauko, kasa,Pipkin ne, ya matsawa maryam sai ta,zo su yi game, Wayan tai yai kara ta dauka don ta diba, wa ANTYNA tagani an rubuta baro,baro, Mamaki ya kamata,saboda ganin kiran wace tadade tana mamakin rashin kiran ta, Anty tafadi a,lokacin da ta dauki receive din wayan nata, Maryam ya kuke ya mai gidan naki, saida maryam ta lumshe idon ta saboda wani farin cikin da ya ziyarci zuciyar ta, don yau taji dadin sautin muryan yar na ta, A lokacin Yusuf ya karaso falon cikin shigar shadda assh mai haske, Ganin yadda maryam take waya acikin jin dadi yasa shi mamakin koda wa take wanan wayan, Cikin dan murmushi yaga tana miko mai wayan, cikin jin dadi, Karba yayi yasa a kunen shi ya mai yin sallama cikin tatausar harshe, Muryan anty yaji tana mai sheri ce mai baban baby, Sun gaisa da murna dajin dadin adduan shi yakarbu na , Yamikawa maryam din sundayi hira take fadawa anty cewa ai anbata bed rest ne yanzu haka A nan Anty taima maryam din warning akan don Allah ta kula da kan ta sosai, Dadi sosai maryam taji na kula ta da yar uwan ta tayi yau din, Abinda tunzuwan ta Abuja aure bata samu ba daga gare ta, Duk irin wahalan da maryam ta taso aciki bata taba nuna gajiyan ta ba, Wai sai yanzu ne yar uwan nata zata bata baya, Dadi sosai ya rufe Maryam din bayan sun gama waya har Safiya saida tai mamaki, Nan tace nikan nasan cewa da akwai abinda yafaru da farko kin ko ga yadda ranan Anty ta rufe ido ta zazaga min masifa cewa wai ai taji Dake dani mun hada kai sai munga bayan auren ta Saboda ina son auren mijin ta na saki a hanyar cuta mata, Kuma kince wai duk tazo gurin ki bidan abu bayan bautan da tai tasaki agidan ta sai kin mata wulakanci, Don yanzu kinfi karfin ta, babu abinda zata iya gwada maki arayuwa, Daga maryam har Yusuf saida sukaji wanan maganar acikin ranan su, Maryam kan hawaye ne yadan zubo mata saboda bacin rai, Yusuf wanda ke shirin fita mai gadin shi yashigo yana ce wa ogan nashi yanada bako awaje, Umar sultan ne yazo gidan motar shi kawai zai isawa mutun shi wani ne Sun gaisa dashi inda yaiwa maryam text zai shigo da bako yanzu, Da sauri suka hau saman stari koda suka shigo basu afalon sai Pipkin kawai, Abin sha da motsa baki aka kawo wa Sultan din yana cine yanaba Yusuf labarin bayan rabon su, Bai boye ba yace kuma yana ganin cewa alakar su zai tashi don dai shi kaunar matar shi da yagani yake so, Dariya Yusuf yai mai yake cewa ai baza ta iya zana dashiba da matar shi baturiya, Nan yake fadawa Yusuf matarshi ta yi accident ta rasu tabarshi da yarinya yar shekara uku, Yusuf yaji tausayin shi sosai inda yai mai gaisuwa mutuwan matar, Umar yake fadawa, Yusuf cewa mahaifin shi da yan uwan shi yanzu sun sa shi agaba sai yadawo gida yai aure,,,,,,,,,, ZEEEE MAKAWA YELWA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣8⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI, ADADE A,NAYI SAI GASKIYA 👍👍👍 GODIYA DA YABO SUN TABBATA GA ALLAH UBANGIJI SUBBAHANAHU WATA,ALA, KARIN GODIYA DA YABO GA SHUGABAN HALLITA ANNABI MOHAMMAD S,A,W,, ALLAH MUNGODE MA DAKA TARAMU A WANNAN GIDAN MAI ALBARKA NA TSAWON SHEKARU BIYU CIF CIF YAU, 👏👏👏👏 KOMAI AKA GINA AKAN GASKIYA GASKIYA CE TAKIN SHI TABBAS GROUP DIN MARYAM SALISU MAIDALA GROUP MAI ALBARKA ACIKIN GROUP DIN HAUSA,,, HAPPY TWO YEARS ANNIVERSARY 🎂🎂🎂 MARYAM SALISU MAIDALA GROUP👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Maryam cikin ga yadan turo izuwa yanzu duk wani kasala da nauyin jiki da take fama dashi yanzu ta daina jin shi,, Izuwa yanzu tai wani girma komai najikin ta ya bunkasa gwanin ban sha,awa, Gata yanzu duk inda jeri mata masu jida kan su suke maryam takai wanan gurin, Ba komai dama ke karawa mace aji ba na farko shi, ne Wadatan mijin ta indan har miji nada wadata shine ke sa mace tai saurin murjewa, Bawai ana nufin wadata mai karfi irin na su Yusuf ba,aa,a Duk irin wadan tan mai gida idan har mace zata samu agaji daga gare shi zaka ga matar rayuwan ta ya nuna cewa akwai shi, Nabiyu kuma ita mace musam man matan yanzu zakaga cewa matan na kokarin su fi maza bidan abin rufin asiri, Wanda hakan wani sabon rayuwane wanda boko yajawo acikin al,umman hausawa,,,, Ganin cewa maryam ta samu lafiya sosai yasa Yusuf sakin jikin shi yanzu duk inda yake hankalin shi a kwance yake,, Saidai kam masu kamfani median na cin riba dasu don ko da yaushe suna makale a waya, Ana faman tambaya may kikeyi Maryam, ? Maryam kinci abin,? Maryam kinyi sallah ko, ? Maryam bakyajin komai dai ? Wanan shine aikin idan Yusuf yana gurin aiki ko yai wani tafiya,,, Bukin chrismas yazo don haka kamar yadda Mr Emanuel ya umurci dan shi da cewa duk Christmas dole yazo gida ayi shi dashi, Shiri sosai Yusuf keyi amma bai sa maryam a cikin tafiyan ba, Asalima dai ita bata ko san da zancen zuwan shi bukin ranan haihuwan Isah almasihu ba,, Wanan akidar haka akasarin iyayen da diyan su suka musulunta suke sawa diyan su wanan dokan, Ko kuma suce akwai family meeting wandai yai dadidai da wanan lokacin, Hakan zai sa dole musulman diyan su su zo gare su suyi wanan bukin kusan atare, Alhamdullahi don ita addinin musulunci addinice mai sauki da fahinta, Addini bai hana musulmi shiga church halatar bukin su ba, Hakan ne yabawa Yusuf daman yiwa mahaifi shi wanan biyayyan don dai yasamu su rabu lafiya dashi,, Waya yake yi da mahaifin shi yana fada mashi irin abubuwan da yake son yaron nashi ya sayo masu, Ruth wace ke tsaye kusa da baban tana zuba mai ruwa zai sha maganin shi, Tace cikin daga murya don yaji ta a wayan, Brother you're coming with your ba,?? Yaji abin da tace sai yai murmushi kawai Mr Ema ya harari diyar nashi yace wetting she go do if she came,? Papa we go celebrated examas with her now,,, Yusuf wanda ke jin su a lokacin idon shi kawai ya iya lumshewa don dai yasan yadace yaje da maryam don duk family su zasu hadu to amma wanan haduwar ta daban ce, May zaicewa maryam din don zuwa da ita cikin yan uwan shi wani matsalane , Gama yadda yasan akidar ta tun tana karama da kyamar masu rashin sallah, Amma bari dai ya gwada yagani idan har zuwan da ita zai zama alheri, Bayan kuma yan church din su Mr Emanuel din suna faman gulman shi cewa , Bana bazai iya bada kyautan da yake bayarwa ba a shekara saboda dama da karfin dan shine yake wanan abubuwan, Yanzu gashi danshi yafi karfin shi ya musulun ta har ma ya auri diyan hausawa ,,, Ita,ko grandmother sai shiri takeyi don har gida akakawo tele ya auna ta, don ai mata din kuno ni, Maryam dai iyakarta da su ido don ba a fada mata ga abinda ke nan ba, Christmas din bana yai daidai da ranan jumma,a ne, Yau tana saye cikin wasu purple din atamfa dinkisu umbrella, yadan matse mata cikin ta ta sama zuwa kasa kuma ya sauko yadan baje iya cinyar ta, Ta daura dan kwali yai mata kyau ga kamshin turen da ta shafa da kuma body spray, tanayi Tabaya Yusuf ya rungumota, inda yasa ta sauke ajiyan zuciya, Wuyan ta yake dan sunsuna a hankali har zuwa kanta, Maryam ta kwanto da kanta zuwa kafadan shi tana sauke ajiyan zuciya, Hannun shi yakai saman cikin ta dan wata shidda ya shafa a hankali, Cikin wani murya mai taushi maryam tace uncle, Yanzu nake shirin zuwa in hada maka kayan ka da zaka dasu, Kara jawo ta yayi zuwa cikin jikin shi, sai,dai wanan karon Juyo ta yayi suna fuskantar junan su yana mai kara kai kanta akirjin shi yace ke kin shirya naki ne maryam, ? Cikin mamaki da kuma sauri maryam ta dago kan ta tana kallon shi, Cikin sauri kuma ta dukar da kan ta don har zuwa yanzu akwai nauyi da yar kunya a tsakanin su, Uncle da ni zaku tafi ne ? Kai ya kada mata alamar eh, Kara noke kan ta tayi tasa hannayen ta asaman West din shi, Habawa uncle shine baka fada min da wuri ba sai yau, A hankali yaja hannun ta zuwa bakin gado suka zauna, Yusuf yariko hannun maryam din yace da farko ina ganin kamar ba,zaki iya wanan dogon tafiyan bane, Sai kuma yanzu naga cewa zan dan dade a can gara kawai in tafi dake don gaskiya bazan iya jure rashin yar matana akusa dani ba, Kunya yaba ta inda har ta dan rufe fuskan ta da hannun ta,, Sosai maryam din tafara shirin ta cikin , sauri daga Anty dije da mahaifin ta har matan shi, Sai kuma mahaifiyan safiya din wace, ita ma an mata na ta kalan tsaraban tare da yaran Anty ta,,, Tunda maman Choima tagane cewa da maryam za ai tafiyan take wa mutane masifa, Don dai ita gaskiya wanan yariyar da ko yaushe take a cikin wanan abin da take ganin matan hausawa musulmai na rufe jikin su dashi,, Sam bata son ganin maryam din a cikin irin wanan yanayin, Yariya karama ta dinga rufe jikin ta ko a gida take ko a waje, kamar muguwa, Ga su da yan matan IBO kuma Christian amma Yusuf ya kwaso wanan yarinyar, da bata da ko fara,a, Yusuf tuki yake a hankali amma hankalin shi na agurin maryam, Bai yarda ko wani driver ya jasu ba,shine ke jan su da kan shi, Shida maryam a gaba suke zaune, maman choima da Pipkin, a baya, Sautin kiraan Sudis ke tashi a motan Yusuf yana bin shi a hankali, Maryam wace zuwa yanzu har barci ya dauke ta ga kuma sa yin Ac da kamshi tana shaka, Maryam bata farka ba sai a tagina daidai lokacin da taji an sake express kwalta, Farka wan ta daga barcin yai daidai da jin aman da tayi,, A gagauce Yusuf yasamu guri ya parker motae sh, Maryam wace har ta fara aman a lokacin tafito daga gefen dake sai faman sannu Yusuf ke mata, Ji yayi alokacin kamar ya kama mata cikin don irin wahalan da yaga tananayi, Maryam tagama ta dawo saman seat din motar tazauna tana cea wai,O, O Allah, Subbahanallah inji yusuf cikin rudewa azuciyar shi kuma yana da yasanin zuwa da ita dayayi , A rude yake cewa may kike so maryam ko mu tsaya ki hutane, tukun, Cikin girgiza kai jikin ta bata jin karfin shi ko kadan tace No uncle muje kawai , Yusuf baiso ba amma dole tasa shi jan motar a hankali Ita kanta mama Choima itin yadda taga maryam nayi duk sai taji dan tausayin yarnyar a ranta, Amma a fili sorry dear kawai take iya cewa, alokacin ganin jikan ta duk ya rude, Gidan shi ya wuce direct dakowa da komai suna isa yasa maryam tai wanka don taji karfin jikin ta, Barci tayi mai nauyi sai a lokacin hankalin Yusuf yadan kwanta, A cikin barcin da tayi mai tsawo wanda har ya sata mantawa da inda take a lokacin, Jitayi kamar muryan safiya akan ta, Abinda yasa ta bude idon ta a hankali don ta gaskanta hasashen ta, A gefen gadon taga safiya zaune a cikin damuwa, A hankali tadan yi kokarin dagowa daga kwanciyan, Sai alokaci tasan ba ita kadai bace a dakin muryan su Yusuf taji yana cewa ki kwanata mana maryam ki huta pls, Nan zanbar ki da ita ina son zuwa gidan Daddy na ne, Inda safiya take maryam tadan kala safiya tace ya jikin maryam, Murmushi tayi wanan karin mikewa tayi gaba daya ta sauko da kafanta kasa daga gadon, Yunwa nake ji safiya madyam din tafadi haka a lokacin da takai zaune da kyau bakin gadon,, Abinci na nan da aka kawo maku daga gidan Anty, Sosai maryam taci abincin tare da kurban ruwa, masu sanyi, Yusuf yana tsaye yana jiran grandma don su tafi amma sai tace yabar ta nan kawai, Don ba inda zata matar shi mai ciki bata da lafiya in ma har church zata sai ya kai ta daga nan din, Ba karamin dadi Yusuf din yaji ba na wanan karamcin da kakarshi tayi saboda sh, Godiya Yusuf yai mata sai cewa tsohowan tayi don may zai gode mata akan abinda yazama dole tayi, Diyan shi jinin tane don haka dole taba da nata taimakon akai, Muryan Yusuf da su maryam sukaji yadawo ne suke mamaki da murmushin shi ya zauna a bakin gado, inda take yana cewa, Grandmother tace bazata gidan Dadd ba zata zauna a tare da ke ne , Murmushi marym tayi tace haba dai sai dai don kai, Amma nikan ai garny bata zama don ni, yanuna cikin ta da hannu yace amma kin san kina rike da jinin ta ko? Murmushi kawai maryam tayi batare da ta bashi ansannkomai ba, Pipkin ne yashigo dakin cikin murnan ganin safiyan da yayi ,,,, , Hannu ta mika mai tana cewa my friend how are you, Yana kallon ta kaman yana son tuna inda yasan ta acikin haka ya mika mata hannun shi,,,, Yusuf zaune a gidan mahaifin shi suna gaisawa Tsaraban su ne ya gabatar mashi dasu duk sai murna suke yi, Mr Emanuel ne yake tambayar Yusuf ko ina maman Choima ? A takaice Yusuf yace tana gidan shi Zata zauna da matana da bata da lafiya saboda wahalan bin hanya da tayi, Jin haka yasa Mr Emanuel bata fuska azuciyan shi wani hau,shi ne ya kama shi, Sosai rayuwan shi ya baci don har ya kasa boye bakin cikin shi akai, Yarinyar ta yarda ta haihu da kaine,? Tambayar yazo ma Yusuf abazata amma sai ya daure yace wa mahaifin shi, Addini na badon wani abu ake auren mutum ba munayi ne don Idda sunnan ma aikin Allah Mohammad S,A,W, Jin haka yasa Mr Emanuel saurin daga wa Yusuf hannu, alamar ya isa hakanan, Baison jin komai a gamay da addinin Yusuf din don daima kamar yafi Yusuf sanin al,adun musulmai, Daga gidan mahaifin shi ya wuce gidan mahaifin maryam, saidai bai gida yana gurin da yake sana,ar sai,da icce,,,, Yusuf har can ya samu surukin nashi gefen titi ya parker motar shi bayan ya kulle motar ya tsallako gurin da baba yake, Ya kasawa wasu yara icce zai dora su a kai Yusuf ya iso gurin shi ya karbi iccen ya dora yaran, Sai ya rusunna har kasa yana gaida mahaifin maryam din, Mutanen dake gefen titin dama wa yanda ke a tsalake duk sukayo masu caaa da ido, Kowa na kallon yadda mutum mai kudi kuma matashi yakewa malam Audu gaisuwa don ya bashi diya, Daga can nesa wasu gungun mutane ke cewa inda malam bahaushe ne da bazai yi wanan ladabin ba don yana jin kan shi wani abu, Sai wata mata ce ke cewa ai da shi yanzu yafi kowa sanin darajan mahaifi, Don dai su kabila sun san girmama nagaban su balle ma wanda ya baka mata, ka aura, Bencin dake gefe baba ya nuna mai yazauna amma sai Yusuf din yaki zama sam, Daga inda yake tsugunne yake fadawa baba da maryam sukazo amma bata da lafiya amai taitayi a hanya kafin su iso, Baba ya ce ashha asshha da sauki dai ko yadan sosa kai yace ai taji sauki don har taci abin ci, To Allah ya inganta Allah ya raba lafiya inji baba din , Gidan Anty yawuce itama sun gaisa da ita sosai inda sukai ta labaran yaushe rabo aga juna, Ta tambaye shi jikin maryam yace ai dama stress ne kawai ke ya damay ta don lafiya muka fito gida Gobe ai zasu shigo nan zata wuni ai insha Allah don gobe zan dan je wani kauye zan diba shanaye na acan, Yusuf yadawo gida bayan yai sallah magrib da isha,i, Yanzu dai yai aure kuma abikan shi na kwantagora sun da samu matsala dasu, Gida ya koma gurin matar shi da kakan shi da yaron shi Pipkin, Shima zama yayi yaci abinci kadan sannan yai shirin kwanciya barci, Washegari tunda safe safiya tana gidan a tare ya kwashesu zuwa gidan anty sun yi addon cikin shiga ta alfarma, Idan mutum ba ance mai maryam bace ba zai taba gane ta ba, Irin yadda maryam din ta koma kamar wata baindiya, Komai nata sai mutum ya kalla daga jikin ta har suturan jikin ta zuwa kafanta, Sai,dai sun samu anyi wa su anty dije rasuwa a family house din mijin ta, Gaisawa sukayi sai dai anty taji kunyan ganin safiya, tare da maryam din, Batai kasa a kafa ta ba safiya hakkuri batare da ta baiyana komaye ba agaban maryam, Hakkuri kawai taba ta sai safiyan tace ai ya wuce babu komai ko, Gaba,dayan, su ,su ka shiga family house din don yiwa sarakkan Anty dije gaisuwa, Waje suke zaune saboda wani irin zafi a cikin dakin, Mutane ana zaman makoki na gaisuwa ana gulman maryam Kowa sai mamakin yadda tazama classic a lokaci guda, Ita ko maryam zafine ya ishe ta alokacin ga Pipkin wanda bai saba ba ya ishe su da cewa su wuce, Gungun matan da suka shigone ya ja hankalin mutane don hakane al,adan gidan makoki yake yanzu,, Don yanzu, da anzauna hirane kowani gungu zakaji da irin tasu hiran, Wa yan nan matan bakowa bane sai iyalin gidan mahaifin Jibrin gaba dayan su, Daga cikin su har da Sadiya matar Jibrin a cikin su, Kallo guda Sadiyan taiwa maryam da Safiya saida ta tsorata, Yadda maryam ta koma alokaci guda ga kyau ga iya dressing gata acikin shiga ta alfarma irin ta matan manya, Kallon guda da tai mazu tasan sun wuce ajin ta nisa ba kusa ba, Bayan sun yi gaisuwa gungunmutane suma suka samu guri gefe guda suka sa nasu tabarma, Kallon kallon aka koma yi da su Sadiya da,su maryam din, Sadiya wani irin mugun kishine ya rufe mata ido a lokaci guda , Daga inda take zaune takarewa maryam wace ta mike don kiran ta da wata mata tayi kakan su illiya don tagan ta, Sai yau tasan cewa kallon tsoro takewa maryam din ada, Shiyasa da antashi magana sai tace yar kauye ce ya aura ai, Yau sai ga bakauya ta girgiza mata imani sai hade miyau Sadiya munafuka take yi, Maryam din wace cikin ta ya zauna mata dan dagwas tana saye da wani alkyabba saman kayan da tasa wanda ganin shi kawai ya isar ma da sakon shi ga kamshi na tashi, Jakarta ta balle tabawa tsohuwan nan kyautan kudi, saboda ta dade da sanin tsohuwan, Dibi duk kayan jikin maryam mafi qualities ne wani irin kishine ya lulube sadiyan da ta tuna cewa da yanzu itace a cikin wanan uban daula, Gashi su Anty dije da yar uwanta suna ci a garasaba sa,. Sam ta manta cewa suma halarcin su Allah yai masu sakaiyya da shi haka, Don kwai a iwa maryam da yar uwar ta cinfuska wasu daga cikin yan gidan su Jibrin din sukace, Ashe matan dan IBO anzo ne ga kuma karuwa har an samu, Masha Allah sai dai kan yaran ai dole ace masu jikokin Emanuel ko,? Sai daga can uwale ta jefo masu ansa da cewa kodai jikokin Hamana za ace masu uban su dai musulmi ne, ko? Ke yar abi yarima asha kida, Inji wata tacewa uwale da tabasu ansa,alokacin, Ganin uwale , zata ita daidai dasu a birkice a gurin yasa Anty dije fadawa wata gwagonsu, Aiko tsohuwan tafito tadinga masu masifa da cin mutunci, Tace a she hurda dashi baida kyau, ? Gashi ko duk kwantagora babu wanda yakai uban ku cin dukiyan dan gida n Ema mai manja, Don dai da kudin kafiri yatafi makka ko kun manta ne in tuna maku,? Haba dai gwago Kande daga magana zaki fara irin wanan zancen haka,, Kada kikawo min diban albarka may yasa yaron ga dan gidan ku baice bai son aikin da yasamo mashi ba, Bagashi har yanzu ya na cin moriyar shi ba ku ba ai maku gori ba sai ku zakuyiwa mutane Ai gara da ita auren shi takeyi akanta farkin addinin musulunci ko, Sai da akazo a,kaja gwago kanden tana ta faman masifa dasu, Sim sim sukabar gidan cikin jin kunyan irin ta,arnatin da gwago kande tai masu a bainin jama,a,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA,,,, [5/11, 3:29 PM] ‪+234 706 582 0685‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 9⃣9⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI ALLAH ABIN GODIYA RAMADAN MUBARAK👏👏👏👏👏👏👏👏👏 FUREN JUJI ,FUREN JUJI ,FUREN JUJI NASADAUKAR DA SHI GABADAYA GA WAKALE FAMILY, KWANTAGORA ALLAH UBANGIJI YAGAFARTAWA MAGABATAN WANAN GIDAN BAKI DAYAN SU WA YAN DA SUKA RAGE A GIDAN UBANGIJI YASA MASU ALBARKA YA DAUKAKA MASU YASA DUK YAN WANAN FAMILY SU GAMA DA DUNIYA LAFIYA ALLAHUMA AMEEN👏👏👏👏👏👏👏👏👏 Yau, Jumma,a ranan da kowani muslmi mata da maza yara da manya har tsofafi zakaga suna murna, A ranan zakaga kowa ya ci kwaliya acikin tufafi na alfarma, wasu ma zakaga cewa kamar kwaliyan ranan sallah idi ne ranan gare su don har abinci yakeyi na alfarma domin girmama wanan ranan mai tarin alherori acikin ta watau JUMMA,AT MUBARAK,, Cikin ikon Allah sai gashi yau wanan ranan mai albarka ya hadewa mutane za,a sallace ta tare da mutanen AHALKITABI, Suma zasuyi bukin murnan zagayowan haihuwan Annabi isah, atare da mutane, Hakan yasa duk inda kaga musan man babban gari irin kwantagora zakaga duk garin ya cunkushe da mutane kala kala, Kowa da abinda ke agaban shi a lokacin ba mai kallon wani, Hakan ne yasa shima Yusuf yau abin yai mai biyu, Ga Dad din shi na son ganin iyakarshi akan sai yaje gurin addu,a gashikuma yana son ya samu sahun farko kamar yadda al,adan shi yake, Maryam tana barci ya shirya tun da safe shida Granny din shi zuwa gidan mahaifin shi, Shi da kan shi yaja su zuwa Church din ya na zaune batare da ya gabatar da komai nasu ba har zuwa lokacin da suka watse daga morning prayers din, A can gidan mahaifin shi yabar Granny din shi don su yi celebration dasu, Yadawo gida yasamu maryam zaune a dining tana breakfast, Kallon shi tayi cikin mamaki don ganun shirin dake ajikin shi lokacin, Ba boyo yace mata kin tashi ? Kai ta kada mai yana kokatin zamane yake ce mata, Kina barci nawuce in kai su Dad da Granny Church don morning prayers, Gaban maryam ne yaba da dam lokaci guda,nan take fuskan ta ya sauyawa, Church uncle ? Yana kokarin bude kulan abincin dake gaban shi yace eh Church naje, Hawaye ne masu dumi suka silalo mata a lokaci guda jikin ta yana rawa, Ganin yanayi da ta shiga yasa shi mikewa zuwa inda take rungumo ta yayi zuwa jikin shi, Cikin murya mai rauni yace maryam kada ki min mumunan fahin ta pls, Maryam ashe har zaki iya min mugun fatan komawa hanyar bata, Magan ganun da yakeyi ne suka dan sa ta tsagaita kukan ta alokacin, Sai dai ta dago kanta tana kallon shi ido cikin ido yau din kamar wace ke son gane wani abu acikin idon nashi a lokacin, Maryam bakya son in gama lafiya da mahaifina ne ? Don na shiga church a tare da su bashi zai sa in koma Christian ba, Asalima naje don ni da kaina nai mai alkawarin hakan cewa zan zo wanan lokacin, Badon komai ba saidon na fahinci cewa mahaifina yana son ya kureni ne sosai, Maganan da yake ta hango gaskiya atare dashi, Sai da yaga tadan sake yakoma inda yataso yafara zuba abinci, Sosai yake cin abincin shi hakan ya tabbatar mata da cewa baici komai daga abincin su kenan maganar shi gaskita ce, Dashi da Pipkin ne suka shirya cikin shiga ta alfarma zuwa sallah jumma,a, Shadda ce gezenah mai ruwan Assh colour din tazarce kala guda dashi da yaron, Da hullar a hannu yafito yana kokarin gyarawa maryam tana zaune tana waya da safiya, Akan zancen abinda yafaru da su jiya gidan karban gaisuwa, Anan Yusuf din yadan yi picking din zancen ita ko maryam ganin shi yasata dakatar da,wayan tanacewa safiya sai tazo, Ido Yusuf ya kura mata yana son jin karin bayani daga gare ta, Duk yadda yaso jin zancen maryam taki fada mai gaskiya, Bayan tafiyan shi ne Safiya tazo gidan, nan suka zauna tare har dawowan Yusuf daga massalaci, Bayan sallah la,asar maryam tare da Yusuf din suka shirya cikin kaya na alfarma zuwa gidan mahaifin shi, Wanan ne rana na farko da maryan ta je gidan surukin na ta tun bayan auren su, Tsaraban da tazowa Ruth dashi shine ta sa a ledar, don ta kai masu, Sun sami mahaifin nashi tare da abokan shi a farfajiyan gidan shi , Suna ta faman tutila giya suna kekewan dariya kamar wasu kananan yara, Direct cikin gida maryam da mai gidan nata suka shiga hankali maryam yai mumunar tashi a yadda ta gan su, Don ji takeyi kamar a ce ahir ta sheka da gudun saboda irin yadda ta tsora ta, Dafdaf take bin Yusuf din duk inda ya cira kafan shi ta a za nata, Sun sami kanen Yusuf tare da maman Choima wace ke cikin shiga ta alfar ma, Gwiwa bibiyu maryam ta rusun na har kasa ta gaida yar tsohuwan, Ansawa tayi cikin nunawa maryam din farin cikin ganin ta a lokacin, Yusuf ma gaishe ta yayi tare da ce mata ya celebration ? Ruth ce tazo ta baya ta rungumay maryam tare da ce mata My wife so na your face be dis ? Ruth ki sakeni kawai ai nayi fushi dake ne ki,ka wuce batare da kin dawo munyi sallama ba ko, Acikin hausan ta mai surkin yare Ruth tace wa maryam din haba dai wifiry, dina kada ki bari ajimu pls, Ledan da ke a hannu maryam ta mikawa Ruth din tace ga tsaraba na nan , A kwai agogo da cliffs da turare kibawa Samuel, nashi ba yawa, Wani irin ihun murna Ruth ta kwala wanda ihun yai daidai da shigowan mahaifin su, Cikin ran gaji yake dan dodogara sandar shi amna yadan bugu duk da dai su giya yanzu bata kashe su,, Da Samuel da Ruth sai murna sukeyi da ihu cikin murna, Ruth ke cewa I love it, , I love dis gift , Yusuf sai dadin wanan hikimar da maryam tayi yake ji hikimar da shi sam bai yi tunanen yin haka ba, shi, Maryam ce ta mike tsam daga gurin da take zaune har zuwa gurin da tsohon ya zauna, Gwiwan ta biyu a kasa cikin mutunci da girmamawa, tace , Ina wuni baba,? Mun samay ku lafiya, in ji maryam din Kwalban turare da agogo taciro daga cikin jakar ta ta mikawa Mr Ema din cikin yar jin kunya, Mamaki yayi sosai na wanan abin da yariyar tai mashi shi d yaran shi, Inda Yusuf yake ya kalla Yusuf din yadaga mai gira alamar ba ruwan shi, Cikin dan bubuga sanda batare da ya ce wani abuba yace, yane jiki, naki do, so ki ko,? Maryam tace naji sauki Alhamdullahi na gode ma Allah, Jin ta ambaci kalman da ya shafi addini yasa shi saurin murde fuskan shi, A hankali tadaga tabar gurin inda yadan bita da hararan wutsiyan ido , Azuciyar shi ya ce wanan yarinyar muddin tana tare da yaron nan bazata bari yadawo Christian ba, Kowa sai murnan tsaraban shi yakeyi sai a lokacin Emanuel yaga Pipkin wanda ke zaune gefen maman chioma, Grandson come here ya mika mai hannu ya nason Pipkin din yazo gurin shi, Amma sai yaron ya make yaki zuwa gurin Mr Ema din, Mr Ema yace wa dan shi Yusuf akwai, makarantar missionaries da yake son a kai yaron nan bada dadewa ba saboda ya koyi addini tun yana karami, No, No Dad don't metion that again, Kasan cewa yaron nan dan musulmai ne don may za a kai shi missionary school ? Nan mahaifin nashi yace yana nufin cewa ya rike yaron ke nan a hannun shi ba zai kawo shi asa shi a school ba, To Yusuf ya san da sanin cewa society tasan da zaman yaron don haka zasu sashi a schools din su, Don ya zama wani abu a cikin Christianity ya tallafawa na baya, Idon Yusuf atake suka canza kala yace cikin hassala wa mahaifishi kada ya fara yakawo zancen yaron nan ko watan watarana, Don yaro dai da uwar shi da uban shi musulmai ne don may za a ce yayi Christianity kuma, Ganin cewa dan nashi yafi sho points na gaskiya don haka yaja zancen yai shiru, Maryam hankalin ta ya tashi a lokacin ganin cewa itama fa diyan Yusuf su na da iko da su, Har sukai sallama da su suka dawo gidan su gab da magrib jikin maryam din ba karfi, Tunanen duniya da tsoro duk ya damay ta, saboda irin yadda taga yau yafaru a gidan surikin nata Ajiyan zuciya ta sauke a lokacin da tai tunanen cewa, koda wani abu ya cika da ita baza ta ba da diyan ta ba, Zuwa wani akida na Christian da taji yana fada, Kai asalima zatayi kokari ta cushawa diyan ta ra,ayin addinin musulunci ne sosai tun suna yara, Kwance take Yusuf wanda shima nashi kalan tunanen daban ne ya nisa tare da kiran sunan maryam, Maryam din wace tai lamo saman gado tqnkar mai barci a lokacin, Tana jin shi amma bata karba mai ba don tasan cewa yasan batai barci ba, Don yana kallon ta har tai wanka tadan gyara jikin zuwa lokacin da ta hayo gado, Yakara cewa don yasan tana jin shi ansawa daine batayi Sai kinyi hakkuri gaskiya kitayani yaki da yan uwana kafin komai ya daidai ta a tsakani na dasu, Koda yake da wuya ne abin ya daidai ta a tsakanin mu dasu saboda banbancin addini da muke dashi, Sam ni bazan so ace diyana sun yi oda koyi da wani akida na mutane na ba , face kawai sai wanda ke acikin addin islama kawai, Babu komai uncle tafafi a raunane, tare da cewa Allah dai yasa suma su gane gaskiya sudawo hannya, Murmushi yayi na takaici yace hmmm kayya da wuya ne maryam, Ya mirgino kusa da ita ya rungumota ta baya ya dan shaki kamshim gashin kan ta , Maryam ki rike ni amna pls ki rike tankar dan uwanki na jini ki so zurian mu ki basu tarbiya ta yadda ya kamata pls, Ya matse ta gam a cikin jikin shi kamar wanda za a kwace mai ita a lokacin , Daga ita har Yusuf din kuka sukeyi ba maiba wani hakkuri a lokacin, Maryam dince tai karfin halin dan juyawa ta rungumo Yusuf tace uncle kada ka butulcewa Allah ga irin ni,iman da yai maka, Badon komai ba sai don yana son ka da alherin shi ya tsamoka daga kafirci zuwa islama, Idan kace kuka zakai mai ka nuna rashin godiyan ka ke nan agare shi, Don haka ka daure ma duk wani challenges din da zaka gani a gurin koma waye daga both side,pls, Shafan shi ta kama yi cikin kokarin mantar da shi bacin ran da yake aciki, Sai bayan kwana biyu ne maryam taje gidan mahaifin ta don gaida matan uban ta, Umma naganin irin yadda maryam ta koma a take wani kibiyan bakin ciki ya soki zuciyar ta Kishin yadda yarinyar tawaye ta goge ta murje a lokaci guda, Har saida takasa boye bacin ran ta alokacin don duk wanda ke gurin ya fahinci cewa rayuwan ta ya baci, Safiya ta rako maryam din tazo gaida matan mahaifin ta din, Tsaraban turamay da kudi dubu hamsin hamsi ta basu, su biyu, Aiko kamar an kara tunzura umma ne a lokacin don irin yadda ta shiga wani hali, A ranan bayan wucewan su maryam bayan baba yadawo ne rayuwan shi bai mai dadi ba, Don masifa da jidali umma tasa mai wai dama don yai arziki da yarinya yadauke ta ya bayar gidan kafirai, Irin suratan da tayi, wa mahaifin maryam a ranan saida dan dattijon yai kuka agaban iyalin shi, Yadaga hannu sama yana cewa Ya Allah idan har na,bada wanan yarinyar don akan abinda duniyar ke zargina Ya Allah kai ne sheda akai Allah ka isar wa maryama da mahaifiyar ta, Dayar matan baba ne tai karfin halin cewa assaha malam ai basai ka tsaya cewa hakana ba, Don Allah yagani da kanshi kuma yasan dalilin ka na yin haka, Don may har zaka damu da yan bakin ciki, Allah ne yai ma tashi irin baiwan ta wanan hanyan, Aida mitum ya isa shi mai hassadane dasai yaki karban kyautan da akai mai yace bai so , Lokacin da maryam zasu koma ta tsaya garin mahaifiyar ta inda su ma akai masu kyauta ta musam man, Anty Dije ta samawa maryam yan aiki mutum biyu da tsohuwa da yarinya,, Yariyar diyar yar Uwale ce da mijin ta ya mutu yabar ta da yara bakwai shine uwale tai masu wanan hanyar, Ita kuma tsohuwan bata taba haihuwa ba yar uwan dangin mahaifiyar maigidan Anty dije dinne, Yarinyar zata zauna da maryam tankar yar uwan ta ne ita kuma matar yan aikin da yashafi maryam din kawai zatayi a gidan, Sun tsaya garin minna gurin da suka ziyarci gidan su Suleiman, Mahaifiyar shi taji dafi sosai inda take basu labarin irin kokarin dake ga Suleiman din Dakuma irin karuwar da yasamu haduwan shi da Yusuf wanda a yanzu yake ji dashi tankar yayan shi,,, Lafiya lau suka isa Abuja amma a cikin dare suka iso garin inda hurera da zinatu ke ta ware idon su gurin kallon wanan daular da Allah ya kawo su a ciki,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA [5/11, 3:29 PM] ‪+234 706 582 0685‬: Aa🌺🌺🌺🌺🌺🌺 FUREN JUJI 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 1⃣0⃣0⃣ ZAINAB IDRIS MAKAWA YAURI ALHAMDULLAHI RABBIL ALAMIN ARRAHAMANIN RAHIM👏👏👏👏👏👏 YA ALLAH NA GODEMA DAKA BANI IKON KAI WANAN LOKACIN DA HARNA KAI WANAN PAGES DIN, KUSKUREN DA NAYI A CIKIN SA, YA ALLAH KA YAFE MUN 👏👏👏 NASADAUKAR DA WANAN LITTAFIN GA WAKALE FAMILY 212 KWANTAGORA, GABA DAYA SU,, YAN WANAN ZURIN ALLAH YA GAFARTAWA MAGABATAN MU WA YANDA SUKA SAURA ALLA KASAWA AL,AMARIN SU ALBARKA,,,,,👏👏👏👏 So, sai maryam din ke jin dadin zama da wayan nan yan rakiyan nata, Furera da Zinatu maryam ta mai dasu tankar yan uwan ta na jini, Hakan ne ya sasu jin dadi wurin uwar dakin nasu saboda sam shawaran ta da mama furera take yin shi, Ita kuma zenatu tankar kaunar ta na ciki daya don komai cikin saukin kai maryam ke bin su,, Bukin Safiya da umar sultan ya taso ga cikin Safiya yai mugun tsufa a lokacin don haka ba tasamu halartan bukin ba sai,dai dinner da akayi a Abuja ta samu zuwa, Washegari da da yamma na kuda ya kama maryam din, Zaman mama furere a gidan ya taimaki maryam don itace ta,gane cewa na kuda maryam keyi, Yusuf takira da waya acikin cijewa take magana, Yana zaune a office yaga kiran wayan maryam bai bata lokaci ba wurin daukan wayan,yana cewa, Sweet maryam, ya dai, kina lafiya, ? Uncle banda lafiya kawai ta iya cewa ta kashe wayan, Hankalin yusuf yai mumunan tashi dajin yadda maryam tai magana, Kamar yai tsuntsuwa ya taso a lokacin, maman choima duk ta rude saboda irin yadda taga yare suna yi, Amma ga maryam sai in idan nakudan ya cije ta zata murde baki, Addu,a takeyi a bakin ta irin yadda aka koya ma su a islamiyar su, Kafin Yusuf yazo har driver ya kai su asibiti ko don bazasu iya jiran shi ba, Allah ya sauketa lafiya ta haifi diyar ta mace mai kama da ubanta sak, Yarinyar farace tas da ita ga hanci da suma baki wulk kamar na maryam sai dar,daran ido irin na maryam din, Daidai fito da yarinyar Yusuf ya karaso asibitin cikin rudewa amma yana ganin ana mikawa mama furera yarinyar a hannun ta sai ya sake murmushi, Hamdala da istigifar yake tayi a cikin bakin shi har ya karaso gurin cikin rudewa, Maman Choima ta daga hannun ta sama tana cewa press the Lord, Sai kuma ta hau rera wakan yabo da godiya irin nasu, Christian, Yarinyar ya karba ya nufi inda maman Choima take yana cewa mama,mama see my blood today woo, Kara runguma yarinyar yayi a jikin shi tankar wanda za a kwace wa ita,, Kunnuwan ta yakai daidai baki shi yai mata ikama kamar yadda Sunna ta umur ta, Sai a lokacin ne ya dago kai inda mama furera take yake duba sai dai bata gurin, Hakan yasa zuciyar shi gane cewa tana cikin dakin da maryam take a cikki, A hankali ya tura kofan dakin maryam din tana kwance a aaman gado asibiti, Idan badon dan fadawan da tayi ba bazaka ce itace ta haifi wanan dirkekiyar yarinyar ba, Murmushi suka sakarwa junan su yana kokarin karasawa bakin gadon ne wata nurse ta shigo dakin dauke da abin allura a hannun ta, Ce masu tayi, da su dan fita daga waje kadan har su gama da ita tukun, Bayan komawn su gidane Yusuf yafara kiran yan uwa da abokan arziki yana sheda masu cewa Allah ya albarka ce shi da diya mace , Daga ciki har da Jibrin wanda suke yar wasan boya dashi, Don tun bayan auren jibrin sau guda suka taba haduwa a massalacin sallah jumma,a, Mahaifin Yusuf ya yi murna sosai da haihuwan da matar dan shi tayi , Har colanut ya raraba abokan hiran shi a church kuma yasa ai mai addun matar yaron shi ta haihu, Kafin wani lokaci labarin haihuwan maryam ya isa gurin duk wanda ke da alaka da ita da Yusuf, Aike na musan man Sonny yaiwa baby da mahaifiyar ta, kayane na baby, Yusuf din wani irin mahaukacin sayayya yayi don har sai da maryam da Anty Dije wace tazo don diba yar uwan ta daga kwantagora, sai da sika ji tsoro, Anty dije tace wa mama Furera ina mazan da ake haifa wa diya mace su dinga butulcewa Allah su zo suga yadda diya mace tai rana agidan Yusuf, Kayan kusan ana iya cika daki dashi aka turo Nigeria, Itama maryam kusan kayan da ya saya mata duk na alfarmane sai da ta kama hawaye don ganin ga na lefen ta ba ta ko fara amfani dasu ba ya kuma jibgo mata wasu, Surprise din da yai masu shine na canza sabon gida da yai masu batare da sanin su ba, Safiya da mai gidan ta da suke batun ketarawa waje haihuwan maryam ya tsaida su da rabon ayi a gaban su, Mota biyu bus na mata guda na maza yan uwan su maryam suka zo gurin taron suna, Yarinya taci sunan Nafisat, Inda akaci akasha kowa ya koma da abin arziki a gidan shi, Mutanen minna sun zo daga kano Alhaji sambo da kuma malam sunzo taya Yusuf din murna, A gurin wanan taron ne Suleiman ya hadu da Ruth inda suka kulla soyayya mai karfi a tsakanin su, Wasa, wasa kafin a wase magana tai karfi a tsakani, Jibrin wanda yazo amma ya kasa shigo ciki ya gaida maryam sai daga waje ya tsaya a cikin rufa, KB ne ke gwada mai mijin Safiya wanda kwarjin shi kawai ya ishi mutum, Ba suyi wani dadewa ba Safiyan tafito cikin shiga ta kamilar mace inda yaga an bude mata wani irin galleliyar mota tashige baya tana dagawa mutane hannu, Jibrin daga gurin da yaje yawani irin nisawa saboda irin abinda yaji a lokacin, Nan kuma hira ya balke tsakanin su da Yusuf da yafito daga ciki ya samu guri, Tambayar Jibrin Yusuf yayi da cewa yadai mutumi na garin yai maka dadifa kawani boye ba,a ko ganin ka, Murmushi mai kama da yake Jibrin din yayi Kb ne yace ina ko zaka gan shi yana can da yar amaryan shi a kwantagora, Can fa yatare gaba daya bai ko xuwa Abuja yanzu ballr ya ne mi mutane, Dariya itin ta yake din Jibrin ya kara yiwa abokan shi aminan yace, Ai nasan kunsan halin da ma,aikatar mu take ciki bada dadewa ba, ko, Gaba dayan su suka a,a Jibrin din yace ai yayi aure ba ai wani dadewa ba , Customers suka kama wa mutane kaya a border su yi kokari don a sako kayan abin yafi karfin su, Shine yan kasuwan sukayi meeting da cgida sai an sauke wanan commety din na su gaba daya, Yace over tree months zaune kawai nake agida ai ba wani hanyan da mutun income ke shigowa, Yusuf ne ya tambaye cikin mamaki da cewa ya akayi har haka yafaru ban sani Jibrin? Nayi ma wani abu ne, da har zaka shiga wanan yanayin amma banda labari, Wani irin nauyi da kunya ne suka rufewa Jibrin din ido a lokaci guda, yaji nasama ta lulube shi , Amma kuma ya rasa ko may yasa hakan ya faru da shi a tsakanin shi da Yusuf din, Mitumin da ke ji da shi tankar dan uwan shi na jini bai bakin cikin yimai ko wani nashi wani abin alheri, Indai har don auren sadiya ce shi kan shi baiji dadin auren ba saboda Sadiyan kazama ce ta karshe ashe, Bata iya gyaran jikin ta ko gida ko girki bata da time din yi,always tina zaune ko kwance tana charting, Sanan shi kan shi kamar ba mijin ta ba don baida ikon kafa mata doka, tabi, Gashi kuma mahaifinshi duk da auren gida ne tsakanin shi da Sadiyan bai son auren nasu sam sam, Mutanen kwantagora kwanan su uku suka shirya suka koma inda aka bar maryam ita da su mama Furera da Zinatu, Ruth wace sam taki komawa gida a lokacin don ta haukace da zancen Suleiman dan matashi mai tashen naira, Naimat da ta fahinci shirin Ruth itace tai ta bata shawaran cewa idan ta musulunta a saboda shi zai yi hakkuri ya aure ta, Suna zaune a falo maryam tana bawa diyar ta nafisa nono, Safiya takirata tana kuka wai zasu wuce a lokacin, Kuka sosai maryam da safiya suka dinga yi don kamar wa yan da bazasu kara haduwa ba, A haka Yusuf yazo ya samay ta inda abin ya bashi dariya, Yace kukan may takeyi bayan bada dadewa ba zasu je suma, Yana son sai Nafisat ta wayo ne su dan fita wani business da yake son yafara yi na international , Nan yazauna suna lbarin irin mutanen da yagani sunzo mai buki, Ruth ce ta shigo saye da wani buje da rigan na tamfa ke a jikin ta, Irin yadda ta shigo gurin a cikin natsuwa yasa hankalin yayan nata zuwa gare ta, don sanin halin ta da yayi da rawan kai, Ruth ya abaci sunar sister din nashi cikin kulawa abinda yaja hankalin kowa gare su ke na, May ke faru ne nagan ki so wick,? haka may akai maki ?ko may kike so ne pls ? Irin yadda ya rude ganin yar uwar shi a cikin yanayin damuwa yasa kowa dake gurin yin shiru, Kawai sai tasa kuka ta wani zuwa ta aza kanta asaman gwiwar shi, Cikin tashin hankali duk gurin suke amna sai Ruth din cikin kuka tace brother I want change to Islam, Wani iri Yusuf yaji a ruyuwan shi amma afili sai furtawa ya yi da ce wa why do you want to change to Islam ? Ansa tabashi da cewa Suleiman nake son in aura, Yusuf yaji wani iri a zuciyar shi sai furtawa yi da fadin Allahu,Akbar, Kowa gurin yai farin ciki da jin abinda Ruth tazo da shi, Abu guda e yazowa Yusuf a zuciya shine mahaifin su Hakan yasa shi lumshe ido shi, saboda irin rikicin da ya hango za,a yi nan gaba, da mahaifin su, Yadan kira sunan Ruth din tadan dago da jajayen idon ta ta kalke shi, Yace zai kai ta gobe gurin da zata karbi shahada, Amma fa tasan cewa bawai don Suleiman zata musulunta ba sai don Allah da zatawa bauta wa, Kai ta gyada mai alamar to taji abin da yace nan ya fara mata nasiha akan yarda da Allah dakuma dokokin shi, Maryam tana dakin ta kanta babu dan kwali sai dogon gashin kan nata da ta daure shi a cikin ribon yana sheki, Kafanta a mike yake saman gado tana bawa baby Nafisat nono, Zina tuna tsaye daga gefen su tariko kayan da,za,a canzawa baby din don kwanci sai faman lakatan kumatun yarinyar dake ta faman zukan nono, Yusuf yashigo dakin cikin farar jallabiya ajikin shi, Daga massalaci yake tunda zun ya na can zaune, Gashi ya shigo dakin yasa zinatu saurin barin ba dakin muryan maryam ce kece wa zinatu zo ki tafi da ita ma zina, No inji Yusuf wanda tunda, yashi dakin maganar shi kenan ta farko, Hannu ya mika don tabashi yarinyar wace keta faman zukan nonon ta alokaci, Kingama bata koshiba har kina cewa wai a fita da ita waje, Ko nonon na sayarwa ne da ake mata rowa ana bata kadan kadan, Murmushi kawai maryam din tayi ita dai kokarin cire yarinyar tayi a nono ta mika mai ita, Barci yarinyar tacigaba dayi kawai abinta, batare da tasan inda take ba,, Kallon yarinyar yajeyi part by part kamar mai son gano wani abu a jikin ta, Maryam ta mike daga gurin da take ta dan gyara rigan ta da kyau, Kumatun yarinyar yadan lakata yana cewa Sweetyna Kinji aunt din ki ta zatayi sha hada ko albarkacin ki ta sanadinki zata musulunta, Mun fara yawa a cikin family ko insha Allah watara har bazamu iya kidayuwa ba ko, Tun muna furen juji zamu koma FUREN MASSALLACI KO ? Yadan kara lakutan kumatun yariyar dake barci kamar wanda ke fira da babban mutum, Maryam tana daga gefen shi tana kallin su cikin tausayin abin da yake cewa, Gab da shi tadawo ta zauna jikin su na gugan juna tace, Nayi murna sosai da wanan musuluntar da Ruth zatayi dafatan zata shigo da kafar dama, Ya asa da fadar Ameen ya Allah yana mai lumshe idon shi, don jin dadin addun ta ga yar uwan shi, Maryam din tace ta kayi magana da shi sule man din ya yarda cewa zai aure ta, Yusuf yadan murmusa yace ai mun gama,zancen dashi don har mahaifiyar shi munyi magana da ita tasa muna albarka akai, Washe gari ne Yusuf yakira mahaifin shi yaje sheda mai cewa Ruth karbi shahada takoma musulci don zata auri musulmi, Tsohon sai da ya fadi don rudewa sai sambatu yakeyi yana cewa sai yakashe Yusuf, Ruth yanzu tazama Aisha sunan da taci ke nan na musulunci, Daga haka Yusuf bai ja wani lokaci ba yadaura mata aure da masoyin ta Yusuf, Haka rayuwa taci gaba dazo masu a cikkin dadi da ci gaba don yanzu komai yakara bunkasa ma Yusuf, Nafisat yanzu tana da kan nai biyu da Ahmad Mohammed Nasir, Maryam ta zama big madam sosai tana tallafawa yan uwan ta ta hanyoyi daban daban, Gashi kusan duk shekara sai mai gidan ta Yusuf yabata kujeran makka biyar tarabawa dangin ta, shikuma sai yazaba acikkn al,umma Annabi yakai, Kaunar shi Aisha yanzu yaran ta biyu da Suleiman, Naimat tanada yara hudu da ibrahim, Safiya dake can America tare da maigidan ta itama yaran ta biyu duk ka maza, Jibrin yasamu Allah ya taimake shi sadiya ita da kanta tace batayin auren, Fitan ta da kwana daya saiga shi Yusuf ya turo yazo an samu wani aiki da zai jaragaman gurin, Aisha yanzu duniya yabata baya sosai don girma ya kamata ga yan matasan yan mata nan ba a yayin su, Tana son aure amma ba taruhin kwarai arayuwa kowa gudu yajeyi, Gida mai kyau Yusuf yaiwa mahaifiyar maryam da maigidan ta acikin kamfanin bobi, Shima baba duk an buge tsohon gidan shi anyi mashi wani plat mai kyau na zamani, A, A da kan shi yazo har gidan Yusuf don ya taimaja mai yasa mai hannu a takardan wani company nasu, Inda yaga yaran maryam a fola nan taje yaji wani iri a rayuwan shi, Assalam da Issalam yazu ko yaushe suna gurin little mum din su don ma shi Assalam kusan a can yake zaune, Watara aka bugo masu waya cewa Mr Ema a asibiti ya kwana don haka gaba daya gidan su ka kwasa sai Kwantagora, Sun samu yaji sauki don hawan jini ne ga kuma tsufa, Ganin yaran uku yasa shi murmushi da jin dadi daga gadon asibitin, Daya baya yake gaisawa dayaran suna mai kiriniya akan shi yana mai jin dadi sai shafan kan su yakeyi yana lumshe ido, Alokacin maryam takaraso kusa dashi dauke da cup din fresh milk tana lalashin shi yatashi ya,sha, Dad yaji sauki don haka bazu koma ba don suna kula dashi yakuma samu lafiya yanzu Waya aka bugo masu daga garin su cewa maman Choima ta,mutu, Haka suka kwasa zuwa gurin bukin rufe ta saidai maryam da yaran ta duk suna cikin shiga ta musulunci, Mutane sai kallon su sukeyi ita da Aisha da Naimat yadda suka bammbanta kan su da,sauran, mutanen gurin sai wani irin kallon su sukeyi, Maryam wace sai kafa kafa takeyi da yan diyan ta inda tadibi yawan yan uwan su Yusuf din mutane masu karamci amma duk ba muslumai bane, Tabbas su Yusuf furen kan juji ne to indan anbar furen a cikin juji a haka zai tabbata har ya gaji da haskawa ya bushe, Amma dazaran anciroshi daga cikin jujin sanu,san sai kowa ma ya manta cewa daga cikin juji a ka ciro shi, Hakan yakara mata son mijin ta tare da yan uwan shi , Sun dawo ba,a dade ba Samuel yasamu kaunar Ibrahim inda shi ma yadage dacewa ita zai aura, Wanan karon Mr Emanuel bai jaba shi da kanshi aba da bakin a yi bukin, Su maryam sune sukayi shugaban cin komai akan sha anin, Inda maryam takara samun wani ciki ta hai yarta mace wace taci suna Dije, Anty Dije yanzu sanar ta yavigaba bisa taimakon Yusuf wanda akan taimakon da tabashi a baya bai mata ba, Har yanzu jinta yake tankar uwa ko babban ya a gare shi, Baba ya tsufa yanzu amna har yanzu yana da halin dattijan takar shi, Duk Yusuf yai mashi slheri sai yai tafada cewa yai yawa yadaina hakana, Yusuf yana tsaye yana kallon wani tarda sai ji yayi an rungumoshi ta bayan shi, Murshi yayi don yasan kowacece maryam ya furta cikin jin dadi, Yace cikin wani irin murya Baki barci ba har yanzu tawani lunshe ido tace taya zan yi barci bayan Furen zuciyana idon shi biyu yana muna fafitar ka neman abin rufin asiri Idon shi ya lunshe tare da dan dukawa ya aje takardun Kamota yayi dakyau zuwa jikin shi yana cew maryam ban da abin dazance sai dai ince Almadullahi Allaqulli halin,,,,,,,,,,, ZEEE MAKAWA YELWA