*** [1/1, 12:35 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 23/10/2023 Monday. 2:18 PM. *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 1* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin Kai, tare da salati ga Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama.* Alhamdulillah yau Yau 23 ga watan 10 shekara ta 2023, Allah ya nufeni da kafa alƙa'amina na fara rubuta sabon littafina mai suna INDA RAI, Ya Allah ina tawassali da kyawawan sunayenka, Allah ka bani ikon rubuta alkhairi a cikin wannan littafin nawa, kayi riƙo da hannayena da rubuta sharri duk ƙanƙantarsa, ka bani hikima da basirar rubuta abinda zai amfanin al'ummar musulmi baki ɗaya, Alhamdulillah Yah Allah ngd maka dama ka nuna min forkon littafin nan Lfy. Ya hayyu ya ƙayyum bi rahamatika astagis, ka nuna min ƙarshe littafin nan Lfy dani da masu karatun baki ɗaya,Yah Allah ka nuna mana forkon littafin da tsakiyarsa da ƙarshensa dama duk wani sashi da layi da ɗigo na cikin littafin nan Lfy. Yah Allah kayi riƙo da hannayena da tunani da yatsuna da rubuta abinda zai zame min masifa ko wahala ko tozarta na nan gidan duniya da ƙiyama. Yah Allah gamu gareka kaine mai rawaya, mai kashewa, mai badawa, mai hanawa, Yah Allah ka rayamu bisa imani kan tafarkin Muslunci da bin dokokin shariya, Rabbi ka azurtamu da lfya, da imani, da wadata, da kwanciyar hankali, da zaman lafiya, kasa muyi kekkyawar rayuwa, ka bamu kekyawan karshe, kasa mucika da imani, da kalmar shahada, ka sadamu da mala'ikun rahama yayin fita ranmu, ka sauƙaƙa mana amsa tambayoyin Qabari, ka yalwanta mana makwancinmu ka faɗaɗamana, ka haskaka mana, ka ni'imta mana, ka ƙamsashamana, ka sayan ƙaburburanmu su kasance dausayin Jannatul Firdausi, damu da iyayenmu da ƴaƴanmu da yayunmu da kannemu, da kullum musulmi. Ya rabbil izzati ka samu ƙarƙashin inawur al'arshinka a ranar da babu wata inuwa sa ita, badan mu ba, badan ayyukan muba, Yah Allah sai dan rahamarka da ƙaunarka garemu, Allah ka sauƙaƙa mana tsallake siraɗi,😭🙏🏻🙏🏻🙏🏻. Yah Allah kasamu cikin al'ummar Annabi amintacciya. Yah Allah mu bayinkane masu yawan zunubai, sai dai hasken gafararka da rahamar ka ya rinjayi duhun zunubanmu, Yah kayi mana gafara da rahama ka shafe zunubanmu. Ka shiryemu bisa tafarkin gaski ka ɗaurar mana da imaninmu a zukatan mu, Yah Allah kada ka jarabcemu da ƙaddarar Jarrabawar da zata raunata mana imaninmu bare ya rabaku dashi. Ya Allah ka azurtamu da halal, ka nesanta haram daga garemu. Yah Rabbi mu ma buƙatane a gareka kai kuma mai badawane da baya yankewa. Yah Allah masu lafiya, ka ƙara mana Lfy da imani, marasa lafiya ka basu lfya da imani, masu ciki Allah ka sauƙesu lafiya, masu son haihuwa ya Allah ka azurtasu da nagartattun yara. Yan Allah mu masu Yara Allah badan halinmuba Allah ka shirya manasu ka tsaresu da sharrin akiruzzaman, Yah Allah masu neman mazan Aure Allah ka azurtasu da maza na gari, maza masu neman aure ka azurtasu da mata na gari. Yah Allah masu son zuwa aikin hajji da niya, Allah ka kawo mana sauƙin rayuwa da rogomin farashin komai na rayuwa ka bamu ikon zuwa Hajji kasa muyi Hajji Mabrooq, Yah Allah yan uwanmu musulmai dake Palastine Yah wahidulqaharu, ka shigar musu faɗanan ka tozarta waɗanan baƙaƙen kafuran Yahudawa da basa son ci gaban addininmu. Yah Allah ka shiga tsakanin nagari da mugu. Yah Allah ka kawo mana sauƙi da ƙarshen yan ta'adda dake addabar ƙasarmu Nigeria, Yah Allah ka karemu damu da maƙotanmu, musamman Niger, dama duk Afirka baki daya da duk inda musulmai suke a faɗin duniyar nan. Amin Amin Ameeeeeeeen Ya rabbil izzati. *Littafin INDA RAI, na kuɗine, kuma nawa ne ni AYSHA ALIYU GARKUWA, hakkin makalarsa nawa ne, ban yardaba ban amince ba, ban lamunceba, a juya min labarin littafina ta ko wacce sigar, har sai an nemi sahalewata da yardana... idan na amince na bada dama sai ayi. Zama Lafiya yafi Zama ɗan sarki barin haƙƙin wani shine zaman lfyar tauye haƙƙin wani kuwa ko ka zauna Lfy a duniya tofa kasan/kinsa/kunsan gida biyu Allah yayi mana.....!* *Yah Allah ka jiƙan mahaifinta, Faɗimatuzzahara, Rabbi kayiwa (Dedde na) Rahama da gafara alfarmar Annabi da Alqur'ani, Yah Allah kasa mutuwa hutuce a gare ta. Da ita da Yah Abubakar na da Kakata Ayshae, Innayi na, da kakana M Muhammad Babayo Maiturare da kuma Muhammadu Daniya. Da ma dukkan yan uwana Amin Ya Allah* _Wannan littafin sadaukarwane, ga ɗaukacin ƴan uwanmu musulman ƙasar Palastine da aka kashe Yah Allah ka jiƙansu kayi musu rahama ya hayyu ya ƙayyum ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai ka ƙasƙantar da Kafirci da Kafirai._ *Littafin INDA RAI na kiɗine 1k ne kacal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276 mutan Niger ku kuma 1000fc ne wato kaka ɗaya kacal ta wurin Mommy zaku biya +22790899076. Please mommy babbar macece dan Allah mu girmama shekarunta.* Adamawa Yola. Yau garin an tashi da tsananin sanyi mai ratsa jiki da ɓargon ɗan adam, sanyine kuma irin na damuna, wanda aka kwana zuga ruwan saman kamar da bakin ƙwarya, kana aka wayi gari dashi, domin har yanzu karfe 5:00 pm. Ana sassayan yayyafin da ya tsananta sanyi a garin wanda ya tilastawa mafi akasarin, mazauna garin sanya rigunan da zasuyi musu Garkuwa Da sanyin... Yola international airport. Cike yaƙe maƙil, da tarin dan-danzo Mahajatan jirgin ƙarshe da zai tashi daga Nigeria zuwa Saudi Arabia. Gaba ɗaya taron matafiyan, duk wanda ka gani, fuskarsa cike da tarin Alihini, ɗimuwa,gami da matsanancin bugawar zuciya mai cike da Fargana kana da taraddadin mai tsananin gaske, irin fargabar da ɗan takarar shugaban ƙasa da ya binne miliyoyin kuɗaɗe a campaign, yake riskar kansa a lokacin da ake faɗin sakamakon zaben, to irin wannan fargabar maniyatan suke ciki baki ɗayansu. Saboda hukumar amsar jiragen baƙin mahajjata na duniya baki ɗaya, ta fitar da sanarwar cewa, da ƙarfe sha biyun daren yau ɗin ne, za'a rufe KING FAHD international Airport, Saudi Arabia, wanda dama shine ƙarshen rufewa, duk sauran Airports ɗin a rufe su, saboda dafifi da ƙurewar lokacin. Cikin tsananin shiga ruɗu, wani farin Dottijo da bazai gaza shekaru 52 da biyu ba, ya shiga cikin asalin taron Maniyatan, gyaran murya yayi tare da fuskantar su, da kyau a matsayinsa na Amirul Hajj, na Adamawa wanda kuma a shekarar ne aka ɗorashi, yayin da tuni tsagin adawar sa suke farin cikin, ganin a shekararsa ta farko Maniyata sama da ɗari bakwai da hamsin ne bazasu samu damar zuwa Hajji ba. Fuskantar taron ɗaruruwan Mutanen maza da mata, yayi cikin Muryarsa dake cike da rauni, tashin hankali da Karaye yace. “Da forko ina mai baku haƙuri, bisa jinkirin da aka samu na isowar jirgin ƙarshe da zai kwashi mahajjatanmu, zuwa ƙasa mai tsarki. Kuyi haƙuri ku kwantar da hankalinku, kun sani na sani alƙawarin Allah tabbaceccene, in dai Allah ya ƙaddara bana zamuje Saudi Arabia kuma muyi aikin hajji to in sha Allah, sai munje, in kuma Allah yayi bamu da rabon zuwa bana, tofa duk nacinmu da ƙoƙarina wurin ganin hakan ya tabbata bazai yuwuba, so mu maida lamarinmu ga Allah domin shine kaɗai mai iya mana...” Sai kuma yayi shiru tare da zurawa P.A ɗin tsohon Amirul Hajj ido, wanda aka sauƙe, kafin a ɗorashi. Cikin haƙilo,hargowa gami da ɗaga sautin murya mai tattare da kishi ya kalli taron jama'ar tare da cewa. “Na nawa kuma, ai kunga banbancin aikinsa da wanda ya gabata ina tunawa last year, tun saura kwana biyar a rufe Jidda Airport, aka gama kwashe mahajjatanmu, bana kuma gashi duk, Nigeria mune kuran baya, kai Bama Nigeria kaɗaiba duk duniya mune kuran baya, yanzu fa ku duba karfe 5:00 pm. Jirgin namu ma bai isoba bare aje ga batun scaring bare akai ga tashinmu. Gashi a ƙalla mun kai mutum 700 to jirgin da yake dashi da muke tsammanin zuwanshi ma mutum 500 kacal zai ɗauka. Kunga kenan duk yadda za'ayi ma sai mutum ɗari biyu da burbushi sun rasa damar zuwa aikin hajji da kuɗinsu, Amman za'a hanasu zuwa. Annabi yayi gaskiya da yace. Muje tun kafin a fara hanamu zuwa”. Gaba ɗaya al'ummar wurin mgnar sa tayi tasiri a zukatansu, saboda shi maniyacin zuwa Hajji babu abinda ya tsana a duniya, kamar abinda zai katangeshi da tafiya. Wani sashi kuma na masoyan tsohon Amirul Hajj da aka sauƙene suka fara sowar cewa. Bamayin bamayi mai girma Gamna a canza mana shi. Mafiya akasarin maniyatan kuma kuka suke yi sharshar da hawayensu, More especially wadanda shine zuwansu na farko su kam kuka suke harda gunji. Cikin gamsuwa da fusatan maniyatan farin Dottijon dake cike da kamala ya ɗaga musu hannun, cikin tsananin tuhumar kansa da laifi ganin ya gaza wadatarwa mahajjatansu ababen sufuri wasu hawaye ne masu zafi suka fara tsatsfowa cikin jijiyoyin idanunsa. Allah ya sani baya son ya zama sanadin rashin zuwar wasu domin ba mamaki wani in bai je bana ba, babu tabbacin duk zasu kai next year a raye, murya na rawa ya kallesu kana yace. “Kuyi haƙuri mu maida lamarinmu ga Ubangiji mabuwayi gagara misali, in sha Allah, duk zamu tafi, gani nan fa nima kaina ban taf.... Da wani irin sauri duk suka ɗaɗɗaga kawunansu sama. Saboda jin Diri da rugugin babban jirgi dake saukar angulu a cikin Airport ɗin. Cikin sauri wannan Dottijon ya faɗi ƙasa tare da yin sujudushukur kana hawayen farin ciki na kwanta Ya daga idanunsa. Maniyatan kuwa hamdala suka fara yi, wasu na ruggumar juna wasu na sujudushukur ɗin, Aysha ma tana cikin masuyi sujudushukur ɗin. Sai da tayi sujjadar ta godewa Allah, kana ta miƙe tsaye, tare da shiga sahun cikin masu ruggumar juna. Cikin tsananin jin daɗi ta ruggume. Maryam ƙanwar Masoyinta, abin alfahari ta wato. Barrister Kamal Mubi. Itama Maryam ruggume Ayshan tayi cikin jin daɗi tace Alhamdulillah, Aunty Aysha. Allah ya amsa addu'armu”. Cikin jin daɗin Aysha ta sharce hawayenta domin tanaji a jikinta in sha Allah, zataje aikin hajj. Haɗaɗɗiyar wayarta ƙiran Iphone 13 pro ta zaro kana ta dannawa Barrister Kamal kira, bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga cikin tsananin so kulawa yace. “Hallo My dear ya akayi”. Wani amintaccen murmushin da yasa dimples ɗin ta duka biyu lotsawa tayi, tare da lumshe manyan idanunta masu yalwataccen gashin idanun dake jiƙe da ruwan hawaye cikin murya mai cike da haiba kamala da girmama kai tace. “Alhamdulillah Barrister, jirgi ya iso”. Da sauri yace. “Masha Allah, Alhamdulillah Dear sarkin kuka, yanzu dai kuka ya ƙare ko shogoɓatuna?”. Murmushi mai cike da kamala tayi, ta buɗe idanun nata cikin muryar ta da kan rikita kwanya mazaje tace. “Eh Barrister”. Kanshi ya jinjina cike da jin daɗi yadda take mgna dashi cike da biyayya mai gauraye da so, numfashi mai sanyi ya fesar yana mai imagine irin zaman auren da zasuyi yace. “Amman wanne jirgine, badai Arik bakam bane ko?”. Da sauri ta juyo gefen damanta inda farfajiyar sauƙa da tashin jiragen yake, idanunta ta zuba akan tambarin jikin jirgin da aka rubuta Saudi Arabia da manyan baƙake, kana gefe firko an rubuta da harshen larabci. “A'a ba Arik bane!”. “Max Air ne? Ko Kabo? Ko Mangal?". Ya kuma tambayar ta, cike da tsoron kar karamin jirgi aka samu ya gaza ɗiban mutunen duka ya zama tana cikin waɗanda basu samu shigaba. Cikin sauri tabi bayan Maryam da ta kamo hannun tana ja da alamun har an fara Screening. Cike da jin daɗi tace. “A'a Barrister duk basu bane, duk mun girmesu ai, mu a abun masu abun zamu zo, Saudi Arabia Airline ne, da kanshi yazo ɗaukarmu, wani abun saimu ƴan baiwa.” Cikin Murmushin ta ƙare maganar tare da miƙa, ƴar takardar visa inta, aka buga mata tambari, a kai kana ta naɗeshi cikin E passport ɗinta. Haka akaci gaba da tantancewa da yi musu duk abinda ya dace, sauri-sauri gudu-gudu. Domin su samu su tashi karfe shida dai-dai. Dan in sun tashi shida dai-dai ɗinne zasu isa ƙarfe goma dai-dai namu na agogon Nigeria Niger Cemaroon da Chadi wanda kuma zaiyi dai-dai da ƙarfe sha biyu na daren agogon Saudi Arabia, wanda kuma suka bada dakekkiyar sanarwar mai cikekkiyar ikon cewa sha biyu dare dai-dai zasu rufe Airport ɗinsu, sunyi gargaɗin cewa koda one minute wasu suka makara tofa dole sai dai su juya inda suka fito. Alhamdulillah tuni sunyi nisa a komai har Passingers sun fara shiga jirgi. A ɗaya sashin kuwa wanda ake bincikar lafiyar. Pilots and Hostess tuni an gama bincikar lafiyar hostess ɗin kab, an kuma basu duk kulawar data dace dasu domin. Yanzu zasu juya duk da su an sauwaya wasune. Cikin ƙwarewa likitan dake sashi na musamman ya fara bincikar lfyar pilot ɗin da zai juya da jirgin. Sheykh Afif Muhammad Taj. ɗin da abokin aikinsa Pilot Irfan Imran ya sauƙo da jirgin kana kuma zasu juya dashi. Cikin ƙwarewa da iyawa, Doctor ya gama dubasu ciki da waje. A hankali ya jinjina kanshi tare da kallon Sheykh Afif Muhammad Taj yace. “BP ɗinka Nomarl kai komai ma Normal ne sai dai Heart ɗinki na beating so fass yayi yawa, over yana bugawa sosai. Menene matsalar?”. Cikin sauƙe nannauyan numfashi tare da lumshe sexy eyes inshi da tarin gajiya ya ƙara rikitasu tare da ciwon kai daya buwaye shi, saboda rashin bacci, domin tunda watan Zul hajj ya tsaya bai samu cikekkiyar nitsuwaba kasancewar, yana aiki a ƙarƙashin Company Saudi Arabia Airline. Wanda hakan kan sa duk ƙarshen shekara aikinsu kan ruɓanya. Cikin tattausan lafazi da sassayan murya yace. “Hmmm”. Cikin kulawa Dr ya kalli pilot Irfan Imran dake cewa. “Amma ai wannan ba wata matsala bace da zata hanashi aiki, sai dai kanshi na mishi ciwo”. Ya ƙare maganar cikin alamun sanin halin Sheykh Afif Muhammad Taj ɗin, mutum ne shi mai tsananin zurfin ciki ga juriyar ciwo, ya tabbatar bazai buɗi bakinsa yace ga wani abu na mai ciwoba, ko shi sai dai ya gane, da ganin jijiyar goshinsa ya tashi, kana na gefe da gefen kanshi suna harbawa, ga kuma idanunsa da suka sauya launi zuwa ja. Afif Taj. kenan damo Sarkin haƙuri ya kasance Mutum mai tsananin haƙuri kawaici Uwa uba zurfin ciki yana da wasu irin nutsatstsun halayya masu cike da Alkunya sai dai yana da tarin kwarji. Kai Doctor ya jujjuya tare da cewa. “Tun yaushe yake fama da matsalar bugun zuciyar, da ciwon kan?”. Yana mai miƙewa tsaye yace. “Almos 2 weeks yana fama da matsalar”. Da sauri Dr yace. “Ok yanzu kafin kazo, suma can Saudi Arabia sun san da wannan matsalar taka kenan?”. Kai ya jinjina tare da fara tafiya, yana mai kallon time a haɗeɗɗen agogon Diamond na company Gucci dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa. Ganin ƙarfe shida saura kwata ne yasa ya ƙara saurinsa bisa gefen wani ɗan madaidacin gado ya zauna. Pilot Irfan Imran kuma cikin yaƙini yacewa Dr. “Yess Saudi Arabia sun sani, kuma Jordan ma sun sani, hakama Qatar dan, da haka aka bashi izinin tashi a Qatar”. Kai Dr ya jinjina kana yayi saurin bin bayan Taj ɗin. Wani ɗan maganin ya ɓalla tare da miƙa, mishi amsa yayi, ya afa a baki tare da amsar goran ruwan Faron, ya kora maganin dashi, sai kuma ya sauƙe numfashi mai nauyi, tare da buɗe bakinshi, kana ya ɗan ɗaga tounge ɗinshi sama kaɗan, saboda ganin Dr na son saka mishi maganin wanda ya fahimci na ciwon kaine, a ƙasan harshen nasa ya manna mishi ƙwayar magani, in 5 seconds maganin ya narke ya fara bin jijiyoyin kanshi, a hankali ya lumshe idanunsa tare da ɗan gyara kwanciyarsa. Dr da kanshi yayi saurin kwantar da kanshi bisa pillow. Lumshe idanunsa yayi kamar mai bacci, Amman ba baccin yakeba, yana sauraron bugun zuciyar tasane dake lafawa da kuma fitinenne ciwon da ya fara sauƙa. In two minutes yaji bugun zuciyar ya lafa sosai hakama ciwon kai ɗin. Gwaje-gwaje na musamman Dr yayi minshi dan tabbatar da lfyarsa a matsayinsa na mai jan mutum kusan dubu. Murmushi yayi tare da cewa. “Alhamdulillah komai yayi dai-dai zaku iya tafiya”. Jin hakane yasa Taj miƙewa. Tare da gyara wuyan rigarsa. Daga nan suka fito. Anan cikin jirgin kuwa. Alhamdulillah gaba ɗaya passingers ɗin duk sun shiga. Yayinda tuni Hostess sun fara aikinsu, cikin iyawa da kwarewa. Suke rurtufe durowowin jirgin, tare da gyara sakalawa passingers ɗin nasu sit belt, domin sanin pilot ɗin na shigowa zasu ɗaga ne. Gaba ɗaya passingers ɗin kowa da irin kalar tunaninsa da muka nazarinsa da abinda yake yi. Mafiya akasari selfee suke buga kamar ba gobe. Wanda Maryam da Aysha ma na cikinsu. Duk da su a first class suka, ta gaba-gaba basu da nisa da gefen matuƙan. Sai hoto da video sukayi ita da Maryam, Murmushi Aysha dake gefen wata ƴar duma-dumar mata mai matsakaici shekaru wacce ke riƙe da wayarta bisa alamu karatun ƙur'ani takeyi cikin suratul Khaff kasan cewar yau ɗin jumma'a ne. Ganin alamun ta dire ayar ƙarshen surar ne, tayi addu'a ta shafa a jinkinta, sai kuma ta ɗan kallesu a fakaice ganin alamun kamar dai baƙin shiga jirgine saboda yadda suke ta kabta selfee ba ƙaƙƙautawa ɗan gajeren murmushin dake nuna alamun sakin fuskantar tayi tare da ɗan jingina kanta da kujerar ta kalli gefen dama inda Aysha take, tana kallon baiwar kyau da haiba da Allah yayiwa Aysha ga tarin kwarjini, haka nan taji tana burgeta saboda Aysha mutunce mai shiga rai lokaci ɗaya, ga kwarjini tana da yanayin nan da in mutum bai san taɓa zauce tana da girman kai, sai dai bawai girman kai bane, girmama kaine in an zauna da ita kuma zaka gane nagartar halayyar masu sawa a sotane. Cikin mutuntawa Aysha ta kalli Kamilar matar da har zuwa lokacin fuskarta ke dauke da sanyayyar murmushi kana tace. “Hi”. Still da murmushi afuskar matar ta ɗan gyara zaman wayar ta tace. “Assalamu alaikum”. Cikin lumshe ido Aysha tace. “Afwan madadin inyi Miki sallama nace, Hi”. Tana mai kallon Aysha tace. “Ba komai dama nayi Miki hakane dan tunasarwa”. Kai Aysha ta jinjina tare da gyara zamanta, kana tace. “Sunana Aysha Abdullahi Matawalle”. Itama matar Murmushin tayi tare da cewa. “Ni kuma Aysha Aliyu Garkuwa”. Cikin sauri Maryam ta ware Idanunta tace. “Laah Aunty Garkuwa, , kai yau gani ga Garkuwa, duk da muna ƙasa ɗaya gari ɗaya Amman ban taɓa ganinki ba, sai gashi cikin ikon Allah yau tafiya ta haɗamu”. Murmushin Garkuwa tayi wanda ke nuni da karamci da kula ga duk wani Masoyinta tare da kallon Aysha da ta fara yi musu video tana cewa. “Bari inyi mana video”. Tafin hannunta tasa ta ɗan kare fuskarta tare da cewa. “Ya isa haka, muyi addu'a za'a tashi yanzu”. Kai Maryam ta jinjina. Ita kuwa Aysha Matawalle wani sabon video ta fara cikin nitsuwa da maɗaukakin jin daɗi take mgna. “Hi Barrister wannan video en nakane, kaga yanzu zamu tashi, ance 6:00 pm zamu tashi yanzu saura One minute mu tashi, ka samu a addu'a Allah ya kawomu lfy muzo mu sameku lfy”. Sai kuma tayi saurin juya wayar ta gefen window sit ɗinta. Tare da zurawa harabar Airport ɗin ido. A ranta take cewa. Laaa ashe jirgima kamar mota yake tafiya, da tayoyisa a ƙasa yana fesa gudu, ikon Allah. Ita ma Maryam window sit ɗinta take leƙawa. Haka dai kowa da abinda yake yi cike da farin ciki zasu ziyarci ƙasa mai tsarki. Cikin sauri Aysha ta tasa wayarta a Airplane mode, saboda jin ɗaya daga cikin Hostess ɗin na ce mata, ta kashe wayarta. Haka yasa ta ɗan kife wayar bisa cinyarta tare da gyara zamanta kana ta gyara saƙala Aepeace ɗin dake kunneta, tana mai jin waƙar IN DA RAI, na sani akwai rabo yana zuwa. Haka yasa ta gyara zamanta tare da sauƙe sassayan numfashi tana mai hamdala a ranta tare da tariyo dukkan tarin buƙatunta domin wakar kan sosa mata taɓon ƙaddararta. Yess ai dama in dai da rai akwai rabo duk zafin ƙaddaarka bazaka cire tsammanin warakaba, numfashi mai sanyi ta fesar tana mai mgnar zuci tace. “Alhamdulillah oh Yah Allah na gode maka, yau nice Aysha zan tafi maka, Yah Allah ka isar damu lafiya, in ganni gaban ka'aba, in ruggumi Ka'aba, in faɗi tarin ƙaddarorina da jarabbobina masu zafi da ɗawainiya da rayuwata inyi addu'a in sha Zam-zam inyi tawassali dashi, in har akwai jinnu ko wata cutar dake tare dani dake hanani samun salama da zaman lfya a rayuwar zaman aurena. Rabbi ka yaye minshi. Ka sauƙaƙa min. Jarraba mai zafi, domin Jarrabawar Aure itace Jarrabawar mafi ciwo a zuciyar ƴa mace ba Jarrabawar data fita ciwo sai na cuta. Yah Allah kasa inyi Hajj Mabrooq Allah ka amsa min addu'o'in da zanje, inyi. Yah Allah ka takaitamin matsalar rashin nagartar aure kasa in nayi aure da Barrister sai mutuwa zata rabamu. Yah Allah in dai aurena da Barrister alkhairi ne, Allah ka tabbatar dashi, Yah kasa shirin aurena da Barrister ya tabbata, ko dan farin cikin Mahaifiyata da Mahaifina, ko dan in tsira da zargin mutane dake ganin cewa, nice naƙiyin aure.” Wannan sune maganganun zuci da Aysha takeyi. Dai-dai lokacin kuma tayoyon gaba na jirgin ya fara rabuwa da ƙasa, alamun yanzu zasu ɗaga kenan. A can gaba kuwa wurin pilots ɗin, cikin natsuwa da tsanantan bugawar da zuciyar da Taj keyi, yaci gaba da saita komai na tafiyar, yadda kawai zai zauna ne, yana kallon na'urorin ba tare daya taɓa komai ba, muddin sun ɗaga sama. A can bayan kuma wurin passingers ɗin. Cikin sauri sababbin fara shiga jirgi duk suka rurtufe idanunsu kowa da addu'ar da yakeyi. A gefen First class kuwa. Da sauri Aysha ta matso gaban kujerar tare da kife kanta da jikin kurejar dake gaban tata kujerar wanda Maryam ce a kai. Cikin tsananin kaɗuwa da tsoron da mafiya akasarin mutane sukeji a shigan su jirgi na farko. Rumtse idanunta tayi da masifar ƙarfi lokacin da taji jirgin ya rabu da ƙasa baki ɗaya, ferfelan sun fara aiki na musamman damonin tare iska dan saita hancin jirgin wanda , haka yasa jirgin ke marisa irin dai ƴar marisar nan da manyan jirage keyi in sunzo tashi, dan nasu baya kai na ƙananan jirage irinsu... Saurin ƙanƙame saman kujerar da Maryam ke kai Aysha tayi tare da riƙewa saboda wani zuuummmmm da taji jirgin yayi tamkar zai rikito ya faɗo ƙasa, wanda hakan yasa taji zuciyarta ta bada sautin zummmm ɗin har takeji kamar hanjin cikinta na barazanar ɓarewa, ya Salam Aysha Farar kura ga tsoro ga ban tsoro. Wani irin karkarwa jinkinta ya fara yi tamkar mazari, saboda azabebben tsoro da tsinkewar zuciya. Kar-kar haka jinkinta ke rawa cikin tsananin kiɗima ta fara. Karanto duk addu'o'in dake zuwa zuciyarta da bakinta. Da tsananin ƙarfi ta rumtse idanunta lokacin da jirgin ya danyi juyin ɗaukar asalin hanyarsa. Kiɗimarta da diriricewarta ta tsananta ne saboda jiyo wata babarbariyar dake sit ɗin gaba da na Maryam ta zurma wani irin gigitaccen ihu, da addu'o'i cikin harshen barbarci take cewa. “Wayyyo Allah hanjina wayyyyyoohhhh zamu faɗi fa”. Garkuwa kam murmushi mai ɗan sauti tayi, saboda tuno yanayin da ta shiga lokacin forko da ta fara shiga jirgi. Sai kuma ta kalli Aysha dake wani irin karkarwa jinkinta baki ɗaya tsuma yake. Hakane yasa ta yunƙura da sauri alamun zata tashi, sai kuma tayi maza ta koma ta zauna saboda Hostess ɗin dake nufosu da tayi mata alamar ta zauna. Zaman tayi tana mai kallon Aysha yayinda ita kuma ƴar matashiyar balarabiyar ta tsaya gaban babarbariyar nan, tare da zama gefenta ta ruƙo hannunta tana mai kwantar mata da hankali. Aysha kuwa zuwa yanzu ta saki duk inda ta riƙe saboda jin yadda suke marisa a sama yasata, fara fuzgar numfashinta dake kubce mata. Shike nan ashe tsananin son zuwanta Makka da takeyi, shine silar rayuwarta, tunda gashi a jirgi zuciyarta zata buga ta mutu, ashe burin iyayenta bazai cikiba, ashe abinda take tsoron mutuwa ba igiyar aure a kanta shi zai sameta, Allah sarki Barrister yana jiran mu isa ashe ni kam bandani. Sai kuma maganganun zuci da takeyi suka kafe mata, saboda wani zuuummmmm da taji kamar jirgin ya tsinko ya taho ƙasane. Wannan yasa ta ƙara ƙanƙame sit ɗin da Maryam ke kai, wacce itama gaba ɗaya tayi zuru-zuru da idanunta. Ita kuwa Aysha ji takeyi tamkar ta ɗaura hannunta bisa tsakiyar kanta, ta rinƙa kwarara ihu da shelanta, a sauƙeta ta fasa tafiyar, toh Amman ta hani kanta da yin hakan saboda sanin ko tayi tasan baza a sauƙanba. “Yah ilahi ya mujibadda'awati.”. Ta faɗa da ƙarfi lokacin da taji jirgin ya harba can sama ya lula alamun ya saita hancin sa bisa da'irar taswirar hanyarsa. Da sauri Garkuwa ta ɓalle sit belt dinta tare da miƙewa, tsaye ta nufi kan Aysha saboda ganin duk jinkinta ya ɗebi karkarwar tamkar wacce aka jonawa wutar lantarki, kana numfashinta nayi off and dawn, bisa alamufa ta kusa suma. Da sauri ta riƙo hannunta tana faɗin. “Hostess help help”. Jin hakane yasa Hostess biyu dake bayansu saurin isowa kusa dasu. Ita kuwa cikin kulawa take jijjiga Aysha dake karkarwa gaba ɗaya jinkinta sai ƙirjinta dake ɗagawa sama da ƙasa. Ɗaya hostess ɗince tayi saurin ɗaga sautin muryata tare da juyawa ta nufi, side ɗin inda suke tana cewa. “Abata ruwa”. Da sauri ɗaya daga cikin waɗanda ta haɗu dasu suna turo, ruwan da zasu fara rabawa passingers ɗin ta miƙata goran ruwar, amsa tayi kana ta juya da sassarfa. A dai-dai lokacin kuma a can cikin wurin su pilot Irfan Imran. A hankali Taj ya ɗan juyu ya kalli abokin aikin nasa kuma amininsa ɗan ƙasar Palastine. Murmushin Pilot Irfan Imran yayi saboda ya fahimci me aminin nasa ke nufi. Haka yasa ya tashi daga inda yake, kana yazo ya zauna inda Taj ɗin ya tashi Taj. Ɗan miƙa yayi tare da rumtse idanunsa, saboda tsananta da bugun zuciyar keyi, fuskarsa ya ɗan shafa, kana juya ya nufi Bathroom ɗinsu saboda zaiyi al'walan sallan Magrib, dan yaga lokacin sallan Magrib ne ya yayi a ƙasar Nigeria ɗin. Jim kaɗan da shigansa, ya fito, da alamun yayi al'walan dan fuskarsa dake ƙellin ruwa, wanda babu wani gashi ko ɗan tsilli a saman kekkyawar fuskar tasa face gashin girarsa dana ido. Da ido ya ɗan zuba wani ɗan na'ura mai haska musu abinda ke faruwa a cikin wurin passingers ɗin, Hannun rigar jikinsa ya ɗan fara warwarewa saboda naɗewa da yayi kafin yayi salla. Shiru yayi a tsaye ganin kusan Hostess nasu duk suna tare wuri ɗaya. “Mitsss.”. Ya ɗan ja gajere tsaki a saman lips ɗinshi, ganin sun bar passingers ba ko ruwa bare aje ga ɗan wani abun ci. A hankali ya ɗan daddanan wasu pins ya buɗe ƙofar dake tsakiyarsu da passingers ɗin fist class, wanda kujerar babarbariyar nane firko sai ta Maryam kana ta Aysha. A gefen dama kenan. Ganin shine yasa duk Hostess ɗin mimmiƙewa tsaye, cikin tsananin girmamawa da kiyaye tsarin aikinsu. Maida hankalinsu, a hankali ya haɗe lips inshi da ya buɗe tare da cewa. “What happened?”. Cikin sauri ɗaya daga cikinsu tayi mishi bayanin abinda ke faruwa. Yayin da Maryam da Garkuwa kuwa duk sun kiɗime sai kiran sunan Aysha daketa karkarwar tamkar mazari suke. Juyowa Garkuwa tayi ta kalli bayanta jin ana ce mata ta matsa ga Dr Taj zai duba Aysha. Jin haka ne yasa tayi saurin matsawa, tare da jan hannun Maryam, suka bashi fili. Shi kuwa Taj da sauri ya lumshe idanunsa kana, a hankali ya ɗan sunkuyo kanta, sai kuma yayi saurin datse lip inshi na ƙasa da haƙoransa na sama, saboda wani irin masifeffen harbawa da zuciyarsa tayi tamkar zata ɓallo ƙahon zuciyarsa tayi waje. Ita kuwa Aysha zuwa yanzu dai saura ƙiris tsoro ya sumar da ita, duk da jirgin ya dai-da ta kan hanyarsa. Shi kuwa Taj cikin ƙarfin hali ya buɗe kwayar idanunsa ya tsaidasu kanta, alamunta da yanayin yadda take yi yafi kama da na mai iska. Domin karkarwar da salatin yasa ta sule tayi ƙasa. A hankali yasa hannunsa na dama ya riƙo hannunta na dama. Rumtse idanunsa ya kumayi da ƙarfi kana ya jawota ya zaunar da ita kan kujerar. Kana ya zauna gefen hannun kujerar, tata ba tare da ya saki hannunta ba. Cikin gamsuwa da yaƙinin aljanune a kanta ya ɗan juyo ya fuskanceta da kyau tare da yin auziya kana yayi basmala. Ya buɗe lips inshi a hankali tare da ɗan ɗaga sautin muryarsa ya fara karanto mata ƙebantattun Ayatush shifa na Alkur'ani. Ya Salam shine, abinda Garkuwa Da Maryam dama duk sauran waɗanda ke wurin sukace tare da lumshe kwayar idanunsu, saboda jin wani irin amintaccen zazzaƙan sautin muryarsa da yake rero karatun ƙur'ani cikin nitsuwa da cikekkiyar tajweed mai fidda amintaccen Ghunna, Qalqal, iqlab da idgham hadida Ikhfa'a masu sa zuciyar ko wani muminin mutum da aljan samun nitsuwa. Nitsuwar kuwa harda Babarbariyar nan ta nitsu. Ita kuwa Aysha wasu tagwayen ajiyan zuciya masu nauyi ta fara sauƙe. Lokacin da taji Ya Kawo ƙarshen. Suratul Fatiha Sai kuma taja dogon numfashi jin ya ɗauko, Ayatul-kursy A hankali wani nitsuwa ya fara diro mata, wanda yasa jinkinta fara mutuwa. jin ya fara karanta, Aamanar-rasuulu sai kuma ya ɗauki. Laqad ja'akum A hankali tayi luuuh ta ɗan jingina da gefenshi jikinsa lokacin da taji ya fara karanta. Wattaba'uu ma tatlush shayaɗeenu ala mulki sulaymaan. Zuwa yanzu ta fara samun nitsuwa. Jinginar da tayi da jikinsa ne kuma ya sa wayarsa dake cikin aljuhun rigarsa sulowa ya fito ya faɗi, Dai-dai inda wayarta dake kan cinyartan ya faɗi gefen wayarta Wani ni'imtaccen bacci ne ta fara jiyowa yana diro mata daga sama kanta, numfashin samun nitsuwa ta shaƙa gami da ni'imtaccen ƙanshin turaren jikinsa mai sanyaya zuciya, a lokacin da taji yana karanta. Qulyaa ayyuhal kaafiruun Sai kuma ya ɗaura Qul huwallahu Ahad. Qul a'uuthu bi rabbil falaq. Qul a'uuthu bi rabbin-naas. A hankali ta gyara jinginar ta da jikin kujerar tata yayinda rabin gefen kafaɗarta yake ɗan jingine kaɗan da rabin kafaɗarsa wanda ko ya tashi ma bazata zameba. Ganin hakane yasa Maryam da Garkuwa dama duk sauran kowa ya koma mazauninsa, ganin tayi bacci. Shi kuwa Afif Taj, cikeda taushin murya yaci gaba da kawo ayoyin wasu surorin kamar haka. Suratul isra'i aya ta 81 zuwa 82. Suratush-shu'ara aya ta 78 zuwa 82. Suratus-sajadah aya ta 13 zuwa 14. Suratu aali Imran aya ta 139. Suratuz-zumar aya ta 18. Suratul-ankabuut aya ta 41. Suratul-ahazaab aya ta 22. Kafin yazo ƙarshen tuni baccinta yayi nisa, ta samu cikekkiyar nitsuwa ta falalar Alqur'ani mai girma kenan. A hankali ya ɗan kalli gefen fuskarta kana, ya ɗan yunƙura ya miƙe, yana mai ɗan shafa aljihunsa, sai kuma ya kalli gefenta, hannunshi yasa ya ɗauki waya. Dai-dai lokacin kuma hankali sa. Na kan Hostess ɗin su dasukaci gaba da rabawa passingers ɗinsu abinci da sha. Daga nan sukaci gaba da tafiya, suna keta hazo. Ƙarfe goma dai-dai agogon Nigeria Niger Cemaroon da Chadi wanda yayi dai-dai da ƙarfe sha biyu da minti uku kacal, jirgunsu yayiwa King FAHD international Airport dirar mikiya, dora kuwa irin wacce ba zato ba tsammani domin duk da sun san da sauran jirginsu ɗaya a Nigeria bai hanasu cuku-cukun rufe Airport din ba kamar yadda sukace. Shi kuwa Taj. Da sauri ya kutsa kan jirgin bisa da'irar da suka bashi damar saukan 12:00 duk da kuma ganin alamun gargaɗin da suke yi mishi, hakan bai hanashi sako kai gadan-gadan ba, wanda bisa dole yasa suka fara shirin tarbarsa cikin gaggawa, domin da har sun fara datse na'urarorinsu. Murmushi mai sauti Balaraben dake can cikin dogon gidan da suke iya ganin gilmar koda tsutsace aƙasan wurin ko sama. Ya sani wannan aikin Taj ne, domin matashine mai jini a jika, wanda burin rayuwarsa na duniya pilot, haka kuma babu abinda ke sashi karsashi da shauƙi sama da ya ganshi yana sarrafa jirgi. Murmushin yayi tare da bashi umarnin dirowa, Duk da yasan Taj ɗin zai fuskanci ƙalubalen tuhumar dalilinsa na wuce lokacin da aka bashi da kuma yi musu kutse cikin Airport insu. Sau ƙintama shi ma'akacinsu ne, Amman yasan duk da haka da wuya in bai fuskaci dakatarwaba, bisa gargaɗi mai ƙarfi. A nan cikin jirgin kuma Irfan Imran ne, ya saki wani zazzafan numfashi. Jin gubbbb alamun tayoyin jirgin sun dira ƙasa. Aysha kuwa wannan ƙugin shi yasata rumtse idanunta, tare da ɗauka wayar gefentan tasa a cikin hand bag dinta, sabida jin Garkuwa nace. “Alhamdulillah mun isa lfy”. Murmushi tayi tare da buɗe windo gefentan tana kallon cikin Airport ɗin da yake tamkar rana saboda haske. Zururuuuuuuuuuuu haka jirgin ke fellawa da gudu, bisa da'irar da dama itace ƙarshen rufewa saboda ana tsammanin sa. Mamakin yadda jirgin ke gudu ya cika mata zuciya. A hankali ta juyo ta kalli Hostess ɗin data ɗan daga kafaɗarta tare dace mata. “Yau kinyi babban raɓo, lallai ke mai Sa'a ce Captain Taj Afif ke jan jirgin nan, kin samu taimako na musamman badon shiba da suma zakuyi, tunda ko Doctors inmu sun dubaki matsalarki ta junnuce”. Cikin sauri tace. “Kai nifa banda aljanu kawai tsorone”. Murmushin tayi tare da cewa. “Ke dai ki godewa Allah ki kuma godewa Captain Afif Taj.” Ta ƙare maganar dai-dai lokacin da jirgin ya tsaya gis. Daga nan duk passingers suka mimmuƙe Hostess na bubbuɗe musu durowowin jirgin suna ɗaukan jakukkunamsu, ana buɗe musu ƙofa suka fara fita. Bayan awa ɗaya da daƙiƙu arba'in da biyar, duk passingers ɗin, sun bar cikin Airport. Ƙarfe biyu da minti goma dai-dai, Su Aysha suka isa masauƙinsu. Kamar yadda duk sauran majatta kowa ya isa masauƙinsa. Tuni kuma sun ɗauki niyya kasancewar sunso a ƙurerren lokacin yasa cikin Makka suka dira. A can Airport ɗin kuwa, cike da tsananin mamaki Doctors ɗin dake bincika lafiyar su pilot Irfan Imran da Taj. Suka zubawa Taj ɗin idanu. Domin wannan shine karo na farko da bincikensu ya nuna musu cewa Pilot Afif Taj yana tattare da matsalar matsananciyar sha'awa mai gigitarwa. Dan ma kasancewarsa mutum mai tsananin haƙuri, juriya gami da zurfin cikine yasa sam a zahiri babu alamar wannan matsalar tattare dashi ko kaɗan sai suda na'urori suka nunawa, sirrin jikinsa. Tsuke fuska yayi tare da kauda kanshi. Da sauri Dr Yace “Are you okay?”. Cikin takaicin yadda na'urar ke nuna ainihin yadda bukatarsa ke hauhawa kamar farashi yace. “Yesss! I'm okay!”. Ya ƙare maganar yana amsar mgnin ciwon kan da suke bashi. Daga nan dai sukaci gaba da bincikan lafiyarsa domin lafiyarsa nada mahimmanci a gare su. Sai ƙarfe biyu aka ɗaukesu zuwa masauƙinsu dake gab da harami. A hankali Aysha ta ɗan kalli Maryam tare da cewa. “Ba wayarki bace ke ringging”? Kai Maryam ta jujjuya tare da cewa. “Ga tawa a hannunsa ai sai dai ko in taki”. Ta ƙare maganar tana jawo jakar Aysha dake gefentan gami da cewa. “Gashi”. Ita kuwa Aysha Garkuwa dake fito daga bathroom bisa alamu wanka tayi, kasancewar masauƙinsu ɗaya ne. Sai kuma ta kalli jakarta tata tare da cewa. “Kai ai ni kuma ba hakka ringing na yake ba.” ta ƙare maganar tana buɗe jakar tata cikin mamaki take kallon wayar yess gashi dai komai na wayar irin wayarta ce Amman kuma ba ringging ɗinta bane. Sai kuma ta kalli Garkuwa dake cewa. “Aa ki ɗauka mana, har ta tsinke”. Juyo fuskantar wayar tayi ga mamakinta sai taga hoton. Wata kekkyawar Babbar mace ce, mai tarin kwarjini da haiba kana an rubutu. Fist Love a saman hoton nata,. Sai kuma tayi kasake ganin kiran ya tsinke sai kuma poton gaban wayar ya bayyana. Wannan matar ce a zaune sai kuma Taj da yake durƙushe a gabanta ta daura hannunta a kashi tana Murmushin dake bayyana tsananin soyayyarsa a ranta sai kuma wasu mata dake kewaye dashi. Da sauri Maryam data leƙo tace. “Laaa ikon Allah wannan hoton pilot ɗin nanne fa da yayi mata addu'a ta nitsu a jirgi, Aunty Garkuwa ganifa”. Ta kare mgnar tana nuna mata fuskar wayar. Ita kuwa Aysha jakar tata ta fara laluba wai ko zata jiyo wayarta, jin wayam ba wayar ne yasa ta kalli Garkuwa dake cewa. “Ikon Allah tofa inaga kunyu canjin waya da bawan Allah nan”. Dai-dai lokacin kuma wani....! By *GARKUWAR MARUBUTA* [1/3, 2:13 PM] Fa'izatu Tsohuwa: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 2* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Kayana sun iso lfy. Aikin su ya kankama, komai ya zama Available. Duk abinda kake so a cikin wanda zan sako a nan akwaisu Available, kayane masu zafi da tururi kayane da ban taɓa jibgo kamar su da irinsu ba. Ku matso iyayen amare, da amaren da yayun amare da ƙannen amare da ƙawayen amare, Uwar gidaye gareku, tsakar gidaye kuma ban barku a baya ba, mai jego sabon haihuwa ko tsohon jego wato barden goyo, amarya Budurwa ko Bazawarara duk ku taho kowa da zazzafan haɗinsa, ina araha kam duk ɗan karen tsadan da kayan suka ƙara Amman fa ina hana bashi. Idan kayan ɗa'a kikeso ga number da zakuyi min min da ita 08069423567. *Littafin INDA RAI na kiɗine, yanzu munayin free pages ne, ki biya ki karanta cikin aminci, 1k ne kacal, 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki kuma ta wannan number 09097853276. Ku ma mutan Niger 1000fc ne zaku biya wato jaka ɗaya rak. Ta wurin Mommy zaku biya.+22790899076* Kiran ne ya ƙara shigowa da sauri Maryam ta miƙa mata wayar. Atake hoton fuskar wani kekkyawan dattijo fari ƙal dake zaune a tsakiyar zaratan maza manya da ƴan saffa-saffa wanda sun kai takwas zagaye dashi sai kuma Taj dake gabashin zaune ya ɗaura kanshi bisa guiwowin Dottijon,ya bayyana wanda aka rubuta. Yah Abana. Bisa alamu duk mutanen Ethiopia ne, domin su kalar fatarsu da farinsu ke nunasu a duk inda suke a faɗin duniya wanda kalar ƴan Sudan na ɗan ɗibi da suɗin. Kasake tayi har kiran ya tsinke. Sai kuma ta kalli fuskar wayar ganin babu matakan tsarone yasa ta sauƙe numfashi tare da kutsa kai ta shiga. Wurin Contacts ɗinsa sabida tabbatarwa, da sauri ta fara bin sunayen mutanen da yafi mata kama da sunayen larabawa da rubutun da yafi kama da na larabawa da akayi amfanin dashi wurin rubuta sunayen. Cikin sauri tace. “Tabbas ba wayata bace gashi komai ba nawa bane”. Kai Maryam da Garkuwa suka jinjina tare da cewa bai lura bane ya dauƙi taki wayar ya bar Miki tashi.” Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Ok bari in kira layin nawa in gaya mishi ya mana canjin waya”. Ta ƙare maganar tana sa number ta. Kana ta danna kiran. Dai dai lokacin kuma Afif Taj yayi wani gajiyeyyen miƙa, tare da gyara kwanciyarsa bisa tattausan katifar gadonsa na masauƙinsa mai alfarma, wani irin mayataccen bacci mai gauraye da gajiya yakeji, ji yakeyi tamkar kanshi zai rabe gida biyu, so yake ya watsa ruwa ya sauƙa ƙasa ya tafi Harami, Amman ina bazai iya saboda tarin gajiyar dake tattare dashi. Sassayan numfashi mai sanyi ya fesar tare da miƙa, hannunshi ya jawo ɗaya daga cikin woyoyinsa biyu daya aje akan bedside drower, ya sani Ummenshi bazata yi bacciba har sai taji ya isa Lfy. Haka kuma Yah Abananshi sai yaji sauƙansa Lfy yake samun nutsuwa. Yana mai ware idanunsa da bacci ya fara cin ƙarfinsu ya ɗan shafa fuskar wayar. A kuma dai-dai lokacin Aysha ta kalli Garkuwa tare da cewa. “Wayarfa switch off”. Tana zama bakin gadon ta, tace. “Toh ko ya kashe wayar ne”. Numfashi ta ɗan fesar tare da lumshe idanunta kana tace. “No dama nasa wayar a Airplane mode. Wata ƙil shi baima lura ba wayarsa bane”. Sai kuma tayi saurin jiyowa ta kalli Maryam tare da cewa. “Ni Allah ma ya rufan asiri yasa ba'a jirgin nabar wayata ba”. Sai kuma tayi saurin kallon fuskar wayar jin tana ringing ga mamakinta layinta ne. Shi kuwa Afif Taj, manna wayar yayi a kunnensa yana mgnar zuciya mai haɗe da nazari. “Yah Salam na ɗauki wayar mai aljanun nan kenan na bar nawa a wurinta. Ayyah Ummeei na tayi ta kira kenan bata sameni ba”. Sai kuma yasa hannunsa ɗaya ya jawo ɗaya wayartashi. Yess yasamu kiran iyayen nasa kuma, sai dai kasancewar wayar na silent kasancewar itace, wacce yake yawan amfani da ita, waccar ta wurin Aysha iya Family inshi kaɗai yake kira da ita, a Family inma mafi kusanci dashi. Ita kuwa Aysha a hankali ta amsa kiran, saboda jin Garkuwa na cewa. “Ki amsa mana”. A kunneta ta liƙa wayar, cikin sanyi murya tayi cikekken sallama. Cikin son yakice nannauyan baccin dake danneshi ya amsa sallamar tare da cewa. “Kina ina!?”. Cikin sauƙe numfashi ta lumshe manyan Idanunta masu masifar haske da ƙyalli tare da faɗa mishi sunan masauƙinsu da room number insu, ta ɗaura da faɗin. “Ka ɗauki wayata ka bar, min taka”. Ta ƙare maganar cike da tsananin mamakin to ya akayi ya samu ya cire pin ɗin wayar tata har ya kirata, nazarin nata ya katsene jin yana cewa. “Yah Abana, da Ummeei na sun kira ko?”. Da sauri tace. “Eh Yah Abana da Fist Love ne, suka kira Ummei bata kiraba”. Ɗan gudun numfashi ya fesar kana yace. “Ok kada ki amsa kiran kowa idan an sake kira.” Da sauri tace. “Ton ni kuma waye da waye suka Kirani!?”. Cikin lumshe idanunsa yace. “I don't know”. Cikin fahimtar shi mutum ne mai taƙaitattun kalamai ta ɗan yamutsa fuska tare da cewa. “Please idan Barrister ya kira kada ka ɗaga, in kuma Dadeey na ta kira ka ɗaga, ko Abba na kace musu munyi canji wayene. Kuma kace musu ina lfy”. Cikin ƙosawa da surutun nata yace. “Bazan iyaba”. Yana faɗin haka ya katse kiran, tare da cilla wayar gefe, Kana ya kira Ummei shi da ɗaya wayar tasa. Bugu ɗaya ana biyu ta amsa bisa dukkan alamu tana cikin haramine dan yaji sowan dubban jama'a, wacce tafi ta kullum saboda ƙaratowar ranar arfa yasa gaba ɗaya mahajjata sunata hallara cikin Makka. “Afifff”. Ta ƙira sunansa cikin mabayyaniyar so irin ta uwa da ɗanta. Cike da gajiya kana da magagin baccin yace. “Ummeey na mun sauƙa Lfy”. Cikin jin daɗi tayi hamdala tare da cewa. “Alhamdulillah tun ɗazu na kiraka baka ɗauka ba, Malam ma ya kiraka duk bakayi picking calls inmu ba, kana lfy dai kam ko?”. Tamkar yana gabanta ya gyaɗa kai kana ya ɗaura da cewa. “Alhamdulillah Ummeey”. “Zaka shigo Harami yanzu ne?”. Cewar Ummeey. Yana gyara kwanciyarsa yace. “Sai asuba”. Kai ta gyaɗa tare, da miƙawa Malam Muhammad wayar, amsa yayi tare da kaiwa kunne cikin tattausan lafazi da irin soyayyar nan da bata ɓuya a kan fuska dottijon yayi sallama tare da ɗaurawa da cewa “Abana”. Dan haka yake kiransa, kasan cewar sunan mahaifinsa garesa shi kuwa Afif yana juyawa gefen damanshi yace. “Yah Abana”. Murmushin mai sauti dottijon yayi, kana suka gaisa tare dayi mishi sannu da gaji. Jin yadda muryar ɗan nashi yayi ƙasa sosai alamun bacci ne, yasa ya sallameshi, daga nan sukaci gaba da ibadunsu. Su Aysha kuwa bayan sunyi wanka sun ɗan ci abinci. Suka sauƙo ƙasa kasan cewar masauƙinsu ba nisa da Harami. Daga nan suka fara gabatar da aikinsu. Shi kuwa pilot Afif Taj, lumshe idanunsa yayi tare da karanto addu'ar kwanciya bacci yayi, saboda yana da al'walansa. Yana gamawa ya shafe jikinsa kana ya kwanta tare da fuskantar alƙibla, yana mai tasbihi, cikin second nin da bazasu gaza 23 ba bacci yayi awon gaba da shi. Gaba ɗaya Mahajjata, basu da wani tunanin ko, nutsuwa da ya wuce gabatar da aikinsu. Alhamdulillah kuma komai na tafiya, bisa tsari na addini. Yau kwanasu uku kenan, kuma jibine, arfa. Hankalin Majjata duk na can. Aysha ce dake sanye cikin wani Maroon Abaya mai manyan flowers da yayi masifar yi mata kyau sai kuma Maryam dake ɗan tafiya cikin alamun, gajiya, suna ɗan sassarfan bin Garkuwa, domin, so suke su koma gida su samu su ɗan rumtsa, kasancewar a Harami suka kwana. Cikin damuwa Aysha ta kalli Maryam tare da cewa. “Mutumin nan fa, yauma na kira shi, bai ɗaukaba, nagaji da rashin wayata a hannuna, yau kwana ukufa kenan bai amsa kirana, ko su Dadeey na sai dai muyi waya dasu ta wayarki.” Ta dire ayar mgnar dai-dai lokacin da suka shiga lifter da zai kai su masauƙinsu. “Kada ki damu fa ai dole zai nemeki, dan na tabbatar wayarshi tafi taki mahimmanci, kuma Kinga tashi babbar takice, kawai collor insu ne ɗaya”. Maryam ta faɗa mata cikin kula. Kai ta jinjina tana ɗan lumshe Idanunta tace. “Ni da katin nashi bai ƙareba ai ko a jikina bakiga da wayar tasa naketa kiran su Dadeey naba”. Ɗan murmushi Garkuwa tayi tare da cewa. “Okay Shiyasa tun jiya kika buwaye mu, ashe katine, ya ƙare, da shiru kikayi, kinata bin cike mai waya, da duba abubuwansa”. Fuska ta ɗan ƙwaɓe wanda yasa ainihin kyawun fuskarta bayyana tare da cewa. “Yoh shi mema a wayar tashi ba komai fa. Ko pictures babu sai irin wanda in an kiranshi suke ɗan fitowa a fuskar wayar. Sai dai tarin Apps na Qura'an da hadisai da abubuwa su na pilot, da kuma Doctors”. Kai Maryam ta jinjina kana tace. “Gaskiya dai gwara ya ɗauka a samu a amshi wayar, Kinga cewa Yah Barrister mukayi wayarkin ta faɗine, kuma naji yana cewa zai saya Miki wata.” Tayi mgnar cikin tausayawa ɗan uwanta. Murmushin Aysha tayi tare da cewa. “No nima bazan barshi ya sai min wata ba.” Dai-dai lokacin kuma suka isa masauƙin. Bayan sun shiga, ne suka nufi ɗakinsu. Murmushin mai yelwa Barrister yayi tare da nufosu. Cikin yanayin dake nuna yaƙinin soyayyarsa gareta, ya amshi goran Zam-zam ɗin dake hannunta. “Baby kinyi mana addu'a ko?”. Kai ta gyaɗa mishi tare da nuna mishi Maryam da Garkuwa, cikin mutumtaka suka gaisa kana su suka shiga ciki. Shi kuma da ita a Corridor ɗin suka zauna bisa kujerun dake wurin. suka ɗanyi hira kana ya miƙe suka shiga ciki. Kuɗi ya basu baki ɗaya sun. Kana ya fita ya tafi. Yana fita suka ci abinci da suka shigo dashi kana, suka ɗan watsa ruwa, suka kwanta bacci. A hankali yake kimtsa kanshi, cikin wani tattausar jallabiya fara ƙal, sai kuma hiramin daya saka sky blue daya yafa a saman kafaɗunsa, sai kuma yar tattausar hular fara mai ratsin sky blue ɗin ya murza a kanshi, turaren Hubban shadidan, ya feshe jikinsa, dashi, kana ya zira tattausan silifas, shima sky blue. Bakin gadon ya zauna yana shafa fuskarshi da hannun dama, yana jin alamun tofowar sajen da baya barinshi ya bayyana a jikinsa, dan shi saje baya cikin, ababen da ya damu da bari, dan gani yake zai dameshi. Numfashi ya fesar yana mai tunanin, yana gama aikin, Cheving face ɗin nashi zai fara yi. Wayar Aysha dake kan pillow ya jawo, tare da ɗan taɓa ƙasan fuskantar wayar kaɗan da babbar yatsarsa, Ido ya zuba wa fuskar wayar, cike da mamakin yadda yatsarsa kan buɗa wayar da ba tashi ba. Kauda tunanin yayi tare da kiran wayarsa. shiru yayi yanajin yadda wayar ke ringing Amman ba'a ɗaga ba har ya tsinke. Sake kira yayi a karo na biyu, still ba'ayi piking call ɗin ba, har ya tsinke. Ita kuwa Aysha cikin baccinta da yayi nisa, take jiyo ringing ɗin wayar, sai dai tana farkawa kiran na katsewa. Ɗan tsuka ta ja, tare da gyara kwanciyarta ta cigaba da bacci. Shi kuwa Taj, time ya duba, ganin, ƙarfe takwas ne na safe, yasa ya miƙe tare da zira wayar a aljihunsa, dan Ummeynshi tace tana son su shiga Oriental Abaya House. Dan tana son sayawa yar autarta Zakeeya, wata Abaya data fitineta da kira dominsa. Wannan tunanin ne, yasashi miƙewa tare da fita. Yana tafe yana mgnar zuci. “Wannan ina ta shiga ina kira bata ɗagawa, kada kuma inje masauƙin nasu in samu bata nan, bari dai in fita da wayar, in na dawo in fara zuwa wurinsu in amshi wayata, in bata tata adena takura min rayuwa da kiraye-karayen naci”. Ya ida mgnar tare da shiga ɗakin da iyayensa suke, Daga nan suka shiga ɗakin Addawa, wacce kakace a garesa mahaifiyar Ummeynshi. Malam kuma dama tuni yana Harami. Daga nan suka nufi inda zasujen Ƙarfe goma dai-dai Aysha ta farka, Ido ta zurawa gadon Garkuwa saboda ganin bata nan. Zama tayi a bakin gadon tare da kallon ƙofar bathroom dan jin motsin ruwa, sai kuma ta kalli Kofar shigowa, “Yauwa masha Allah, Aysha kin tashi, Please yi sauri mu fita, ga Uncle Ali, yazo mu fita tare dashi, zamufi zararshi”. Cikin alamun bacci tace. “Wayeshi ɗin”. Tana mai kallon Maryam dake fitowa wanka tace. “Uncle nane ƙanin mamana kuma shine Amirul Hajj namu”. Da sauri Maryam tace. “Kai haba tunda muka haɗu nake ta Miki kallon kamar nasan fuskarki, ashe fuskar shi nake tunawa, gsky kuna kama wlh”. Kai ta jinjina tare da cewa. “Eh haka dai ake cewa Amman ni ban yarda ya za'ayi mace tai kama dana miji”. Ta ƙare maganar tana kamo hannun Aysha tana tsayar da ita tare daci gaba da cewa. “Mu tafi. Yanafa jiranmu yace, shekaran jiyama yazo ya samu, kuna bacci baku gaisaba dan haka yau in tasoku”. Cikin sanyi Aysha tace. “Bari in ɗan watsa ruwa”. Da sauri Garkuwa ta jujjuya mata kai tare da cewa. “Please kifi, kada kice sai kinyi wanka, kafin muyi baccifa duk munyi wanka”. Kai ta jinjina kana tace. “Toh bari inyi al'wala”. Bayan tayi al'wala ta fitone, ta kimtsa, cikin tattausar Abaya Black collor mai masifar sulɓi, tayi rolling kanta da ɗan kwalin, kana ta zura takalmin snicker nevy blue, tare da ɗaukar ƴar hand bag itama nevy blue wayarta ta zura a ciki kana, ta rataya a wuyanta, irin rata yawar nan ta kai duka. A jere suka fito. Cikin kulawa Uncle ya sakar musu murmushi tare da cewa. “Yaran albarka ya ibada”. Cikin jin daɗi sakin fuskansa suka amsa da. “Alhamdulillah Uncle komai lfy Lau”. Kai ya jinjina tare da yin gaba yana faɗin. “Masha Allah”. Suna sauƙa suka samu mota a tsaye driver na ciki bisa dukkan alamu su ake jira. Gaba ya shiga ya zauna, yayinda su kuma suka zauna a baya. Kana motar taja suka tafi. Cikin kula yace. “Aysha ya kewan gida”. Kai Garkuwa ta ɗan jinjina tare da cewa. “Gaskiya dai kam Uncle ina missing su yan uwa sun samu duk kusan ɗakinsi ɗaya suke ni kuma. Ni ɗaya, irin Maman Khairta kam ma tunda nazo bamu haɗuba. Gwara Mami, Maman Sayyid, da Aunty Nanee su mun haɗu.” Sai kuma tayi shiru jin Maryam na cewa. “Toh ba gamu ba, muna ɗebe miki kewarsu”. Murmushi tayi jin Aysha na cewa. “Kuma mu jinki muke kamar yar uwa”. Da sauri tace. “Wallahi nima haka nake jinku”. Uncle Ali kam sai murmushi yayi. Sha ɗaya da rabi dai-dai suka isa bakin. Riyal Abaya shop. A kuma dai-dai lokacin Aysha ta ɗan gyara zaman jakarta, tare da zaro wayar dan duba Time, sai kuma tayi arba da miss calls har biyu, da layinta, da sauri ta kira layin nata. Kasake tayi tana jin yadda wayar keta ruri Amman ba'a dagaba, ƙara kira tayi a karo na uku tana mai sauraron Uncle Ali dake cewa Garkuwa. “Yauwa shiga ku ɗauki duk abinda kukeso, in kun gama ki kirani ki gaya min, zan biya kuɗin kuma zan turo Usman yazo ya ɗauke ku da kayanku. Ya ƙare maganar yana miƙa musu. kuɗi, Dukansu uku kana ya haɗa da cewa. “Wannan ku ajiye ne, Amman na sayayyar da zakuyi, in kun gama kawai kuyi min mgn”. Cikin jin daɗi Maryam da Aysha sukayi ta godiya tare da yimishi addu'a. Da sauri Aysha ta maida hankalinta kan wayar jin, an amsa kira na huɗu data sakeyi. A takaice yace. “Kina ina?”. Da sauri ta ɗago kanta ta kalli rubutun gaban saman wurin tace. “For naw dai Ina Riyal Abaya shop, kaifa kana ina?”. Yana mai dudduba jallabiboyin dake gabansa yace. “Oriental Abaya House”. Jin haka yasa tayi sauri ta kalli Uncle Ali tare da cewa. “Ayyah Uncle dan Allah ta ina Oriental Abaya House yake”. Kai ya dan juyo ya kalleta tare da cewa. “Can kuke son zuwa ne”. Da sauri tace. “Eh Uncle dan zan amshi wayata ne a wurin wani yace min yana can”. Kai ya gyaɗa kana yacewa. Driver su tafi can. Ita kuwa Aysha da sauri tacewa Taj cewa, gata nan zuwa yanzu ya jirata, toh kawai yace tare da katse kiran. Tafiya kaɗan sukayi suka isa bakin shop ɗin da yaci uban wancan da girma da cika da ƙasaitattun kaya harma da tsaruwan wajen. Cikin kulawa Uncle Ali ya kallesu bayan sun fita yace. “Ku kulafa, kada ku tsaya har ku rasa jam'in sallan azahar. Kada ku tsaya sayyaya ku mance Ibadar data kawomu. Ni zan wuce, dan zamuyi gaba dan duba ingancin tantunan mu na wurin arfa”. Cikin girmamawa sukayi mishi godiya kana mota taja ta tafi. Da ido suka rakashi suna jujjuya kuɗaɗen da ya basu suna kiyastasu da kuɗinmu na nan gida Nigeria ya kai kimanin Naira dubu ɗari da ashirin da biyar biyar harda burbushi canji. Ga kuma cewa da yayi su ɗau duk abinda suke so zai turo Usman. “Bismillah mu shiga, dan nasan Yah Usman yanzu zai fara ƙorafin lokacin salla yayi bazai zoba”. Garkuwa ta faɗi haka tana gaba, suna biye da ita Maryam tace. “Waye Usman ɗin kuma?”. Suna shiga cikin wurin Garkuwa tace. “Yayana ne, kuma shine PA ɗin Uncle Ali”. Kai suka jinjina kana suka ƙarasa kutsawa cikin shop ɗin. Suna tafe suna dubu tsala-tsalan Abayoyi na alfarmar waɗanda suke da farashi na musamman. Cikin yabawa Aysha ta kai hannunta kan wata Black blue ɗin Abaya da ta amsa sunanta, tace. “Wow Masha Allah, kinga wannan Abayar”. Jinjina kai Maryam tayi tare da cewa. “Kai tayi kam sai tsada kalli kuɗinta fa, in an juya da kuɗinmu kusan dubu dari uku da hamsin nefa”. Cikin kula Garkuwa tace. “Laa ba matsala wlh, ku ɗauka, kema Maryam in kinga kalar da tayi miki ki, ɗauka.” Cike da poolaku Aysha tace. “Kai Garkuwa haba, ai sai kuma abin yayi yawa, ai akwai kuɗi a hannunmu, kin manta jiyama Barrister ya bamu kuɗi ai wannan sai musa Uncle Ali ya samu matsala a kan kujerarsa”. Da sauri tace. “Wlh da kuɗinsa halal ɗinsa ne zai mana hidima ba da kuɗin ƙungiya ba, kada kuji komai ai shi yace mu ɗauka”. Haka dai tai ta basu baki har suka ɗauka kana suka fara duba Vails kuma. Sai kuma gefen bags da takalma. da sauri Aysha ta zaro wayarta jin, tana ringing. Tana amsa kiran taji yana cewa. “Please dan Allah kefa nake jira, na gaji da zaman wurin ga lokacin salla na ƙara towa, kizooohhh”. Wani irin yam taji saboda yadda ya ƙarashe mgnar da wata iriyar gajiyeyyiyar murya kana kasalalelliya”. Murya a tausashe tace. “Ta wanne side ɗin kake”. A takaice yace. “Side ɗin Dubai jallabiya na maza”. Jin haka ne yasa taja hannun Garkuwa Da Maryam suka nufi can. Tare da ce mishi. “Gamu nan ma kusa da wurin”. Shi kuwa a hankali ya zaro ɗaya wayar tashi ya amsa kiran da kakarsa Addawa keyi mishi. “Tajuddeen wai ina kake ne mun gamafa kai muke jira.” Cikin sanyin Muryasa yace. “Afwan Addawa gani nan zuwa ina duba wata jallabiya ne”. Kai ta jinjina kana ta fara nufo inda take zaton nan yake dan ta lura in ba ta jawoshi ba fitowa zaiyiba, ta rasa menene ya tsai dashi. Maryam ce a gaba sai kuma Aysha yayinda Garkuwa ke baya, Kusurwowin ciki, Aysha da Maryam suka fara lelleƙawa. Da sauri Aysha ta juyo jin Maryam na cewa. “Aunty Aysha gashi nan”. A tare Aysha da Garkuwa suka nufi inda yake, tsaye wani daga cikin ma'aikatan wurin biye dashi a gefe yana tura cart da ya zuba abubuwan da ya tsitstsinta. Kasan cewar yana fuskantar ta inda Aysha ta shigone, yasa sukayi ido cikin ido. Wani irin ɓoyeyyen numfashi mai sanyi ya fesar tare da ɗan buɗe lips inshi kaɗan. Kana ya ƙanƙamce amintattun idanunsa, tare da ɗan kawar da fuskarsh gefe, kamar ba ita yake kalloba, sai kuma yayi ƙasa da kwayar idanunsu, daga kan rumfar sawunta ya fara bi, da kallon dake da ɓoyeyyen manufar da yake tuhuma da neman dalilin daya watsa mishi nitsuwarshi a darare biyu da suka shuɗe. Ita kuwa Aysha bisa takunta mai cike da nutsuwa take tafiya. Ba tare da ya ɗauke idanunsa daga kantaba ya amsa gairsuwar da Maryam keyi mishi, kana ya gaida Garkuwa. Dai-dai lokacin kuma Aysha ta iso gabansa. Nannauyan ajiyan zuciya ya ɓoye cikin ƙahon zuciyarsa tare da sauƙeshi a hankali, kana ya fara ware idanunsa tare da yin sama dasu, har zuwa kan 0 face ɗinta da ya fito ras cikin tarhan da tayi. A hankali ya lumshe idanunsa kana ya buɗe su a hankali jin, tana ce mishi. “Sunana Aysha Abdullahi Matawalle”. Kai ya jinjina tare da maimaita sunan a ranshi a fili kuwa a hankali yace. “Afif Muhammad Taj”. Sai kuma ya ɗan kalli gefen hagunshi da wannan ma'akacin yake, tsuke fuska yayi cike da wani irin ɓoyeyyen yanayi yayi mishi nuni da ya wuce gaba yana zuwa. Da sauri Balaraben ya ɗan rusunar da kanshi kana ya ɗan raɓa gefen Aysha ya ɗan yi gaba kaɗan. Garkuwa da Maryam jallabiyoyi suka fara ɗan tsitstsinta ba tare da sun matsa daga wurin ba. A hankali murya can ƙasan maƙoshinsa tamkar mai raɗa yace. “Yah jiki basu sake tashi ba ko?”. Ido ta ɗan jujjuya tare da cewa. “Nifa lafiyata Lau, kawai tsoro naji”. Ɗan ware idanunsa yayi alamar kin tabbatar? Da sauri tace. “Wallahi kuwa ni fa banda aljanu”. Kanshi ya ɗan jujjuya tare da zira hannun sa, cikin aljuhun jallabiyar tasa. Ita kuwa a hankali ta fara taku tare da ƙara matso inda yake, wayarsa ta miƙa kishi tare da cewa. “Ga wayarka, bani tawa!”. Hannunshi na dama yasa ya amshi wayar tare da zurawa a aljihunsa na dama. Har lau kuma idanunsa na kan fuskarta, Sai kuma ya ɗan matsa saboda wasu matasan India da suka zo wucewa ta gefensu. Sai kuma aka fara kallon kallo, domin su matasan sun shagala da kallon Aysha musamman yadda take ta moi-moi da bakinta tana mgna ƙasa-ƙasa da fillanci. “Haka kawai dan na tsorata a jirgi, sai ka liƙamin aljanu to ni dai Allah ya sani bani da aljanu, masu shima Allah ya rabasu dashi, ni kuma Allah ya ƙareni da wannan fatan naka”. Sai kuma ta juya ta kalli gefentan saboda ganin yadda ya tsuke fuska yayi kici-kici, ganin samarin nanne na gefentan dake kallonta yakeyiwa wani irin hantarerren kallon da dole yasa suka wuce. Sai kuma tayi saurin yin baya kaɗan ganin yana raɓawa gefentan zai wuce sanda yazo dai-dai da itane kuma a hankali yace. “Ni ba fata nake mikiba”. Ya bata amsar da fillancin Ethiopia wanda ta ɗan fahimci abinda ya faɗa, sai dai kuma ta cika da mamakin jin yana fillancin. Shi kuwa a hankali ya tsaya Dai-dai wurin Cart ɗin kayanshi da Balaraben nan ke tsaye, hannunshi ya sanya a ciki ya ɗauko ƴan wasu abubuwa baƙaƙe masu taushi, Gabanta ya dawo ya ɗan tsaya, saboda ta juyo ganin kamar zai tafi kuma bai bata wayartaba. Ɗaya daga cikin abubuwan daya ɗaukon ya miƙa mata tare da cewa. “Kisa wannan, ki kuma kiyaye hukunci sheriya ki daina fita haka”. Cikin rashin fahimta tasa hannun ta amshi ɗaya, ga mamakinta Niƙab ne, ganin hakane yasa ta fahimci manufarsa. Wareshi tayi tare da kaishi kan fuskarta, kana tasa hannun ta ta baya ta ɗaurashi. Shi kuwa hannunsa ya harɗe a ƙirji tare da jingina da jikin kantar yayi irin tsayuwar nan ta gefe ɗaya, ya zura mata idanunsu. Kasancewar bata iya ɗaurawa ba yasa ya ɗan karkace, hakanne yasashi, ɗagowa daga jinginar da yayi tare da matsota kana yasa hannun dai-dai saman hancinta, ƴan tsunsa biyu yasa ya ɗan kamo ɗan saman niƙab ɗin, bai bari ko farcensa ya taba fatartaba. Dai-dai lokacin kuma Maryam da Garkuwa suka juyo kansu a tare. Cikin nazartar yanayin Garkuwa ta zuba musu ido tana nazartan su. Maryam kuwa cikin sauri tace. “Aunty Aysha Yah Barrister nefa, ya kira wai in baki, waya zai tambayeki wacce iriyar waya kikeso ya saya Miki. Toh Amman nace, mishi ai mun gane wacce ta ɓatanma, gashi har munzo amsarta”. Ta ƙarashe mgnar tana kallon Taj da yake miƙa wa Aysha sauran niƙab ɗin. Sai kuma ya kauda kanshi gefe ganin, kallon da Maryam ɗin keyi masa. Ita kuwa Aysha numfashi ta fesar tare da cewa. “Nifa abunan ɗauke min numfashi yakeyi”. Yana mai miƙo mata wayarta yace. “Idan kin saba zaki daina ji”. kai ta gyaɗa mishi tare da amsar wayar. Sai kuma ya juyo da sauri jin muryar Addawa na cewa. “Tajuddeen!”. Sai kuma ta zuba mishi ido dake nuna mgnar zuci da takeyi. Ikon Allah Tajuddeen yau kuma, kaine a gaban mace, har kana gyara mata niƙab. A zahiri kuwa sai cewa tayi. “Wannan ƴar wacce ƙasace? Kuma me sunanki?”. Cikin Murmushin Aysha tace. “Suna Aysha Nigeria ce ƙasata”. Kai ta jinjina tare da amsa gaisuwar su Maryam. Shi kuwa Taj ido ya ɗan tsurawa Aysha jin tana cewa. “Dan Allah ya akayi kake iya buɗe wayata”. Kanshi ya ɗan kauda daga kallon ƙwayar idanunta kana yace. “Da fingerprints nake buɗeshi”. Fuska cike da mamaki tace. “Toh ya za'ayi finger ɗinka ta iya buɗe wayar tunda dai da iya finger ɗina kawai na sai tashi”. Cike da kamala da kwarjini da sanyinsa na nutsuwa yace. “Toh nima ban san ya akayi hakaba”. Da sauri ta jujjuya wayar tata, tare da matsa gefe, haskenta ya ɗauke, ta kuma shiga key, miƙa kishi tayi tare da cewa. “Dan Allah sa mu gani.” Kai ya ɗan juya tare da danna kan babbar yatsarsa. Ga mamakinta sai gashi ya buɗu. Da sauri tace. “Ikon Allah ya buɗufa”. Sai kuma tayi sauri ta shiga Settings, ta sake dubawa da kyau yatsa ɗaya ce, sake canza yatsar tayi tasa ta hagu, kana ta miƙa mishi tare da cewa. “Please sa mu gani dan Allah”. Manna yatsar yayi amman sai bai buɗuba. da sauri ta kalleshi lokacin da taga yasa yatsarsa ta hagu saiga waya kam ta buɗu. “Ikon Allah kenan zanen yatsunku iri ɗaya ne?”. Cewar Garkuwa. Maryam kuwa da sauri tace. “Haka dai na fahimta, Amman abinda bada mamaki kam. Kanshi ya ɗan jinjina tare da miƙa mata wayar sabodo Addawa datasa hannun ta kamo hannunsa tana tafiya. Ba musu ya bita saboda ganin ma'aikatan wurin nata firfita dan lokaci salla ya ƙarato. Sauri-sauri gudu-gudu suka zo wurin biya. Koda aka haɗa lissafi Garkuwa na saurin kiran Yah Usman. Ɗaya daga cikin ma'aikatan yace musu. Taj ya biya musu ai. Ya ƙare fadar hakan da miƙawa Aysha wata jaka mai kyau, tare da ce mata Taj ne yace a bata. Ikon Allah gashi tuni shi ya fita, basuma sameshi a wurinba, bare suyi mishi godiya. Suna cikin haka Yah Usman ya iso, da mota da driver nan suka kwashi duk kayan da suka saya. Da gudu-gudu suka shiga gida ruwa suka ɗan watsa tare da yin al'wala hakama Yah Usman da driver. Daga nan kuma suka taho harami ya Usman na bin Aysha da kallon da yasa ƙanwarsa fahimtar ya ƙyasa ne. Alhamdulillah anyi arfa lfy, aikin mahajjatan ya cika, sai waɗanda suka fara sauƙa Makka ne suke da sauran ziyara Madina birnin ma'aiki. (S.A.W) haka dai akayi ta gudanar da aikin wanda zuwa yanzu har mahajjatan ko wacce ƙasa da suka fara zuwa sun fara komawa. Alhamdulillah su Aysha ma duk sun gama ziyar bankwana. A hankali suke fitowa cikin Rauda, cike da bege da son Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama. Da jin ƙunar barin inda yake kwance shi da sahabbansa. A hankali Aysha ke sharche hawayenta da fingers ɗinta, da suka sha jan lalle, dan yau zasu koma Makka, kuma jibi laraba jirginsu zai tashi in sun koma Laraba kuma, al'hamis jumma'a za'a ɗaura aurenta da Barrister Kamal Mubi yayan Maryam kenan. Haka nan take jin tsananin so da ƙaunar Madina, duk da wani sashi na zuciyarta na cike da kewar ƙasarta Nigeria. Ji take kamar ta ɓuya, katta koma Nigeria. Jiki a mace suka fito, kamar ko yaushe, da sauri, ta tsaya jin Garkuwa na gaisawa da muryar Taj. Ido ya zuba mata cike da tarin tambayoyi ganin tana zubda hawaye, ganin kamar bazata yi mgna bane yasa yace. “Lfy kuwa ko dai jikin ne?”. Cikin sanyi murya na rawa alamun kuka na iya kwabce mata tace. “Ji nakeyi bana son inyi nesa da Rauda, ji nakeyi Madina tafi min ko wanne wurin daɗi a duniya”. Sai kuma tayi shiru saboda sassayan kukan daya kwabce mata. Zuwa yanzu ya fahimci cewa. Ita macece mai rauni, da saurin kuka, ga kuma shagwaɓa da gwaurayen sakalci-sakalci. Garkuwa kuwa, tuni itama idonta ke zubda hawaye, shi kuwa Taj a hankali ya kalli. Side ɗin da su Ummeynshi suke bisa alamu Zam-zam suke sha. Cikin sanyi yace. “Ayyah toh kuyi addu'a Allah ya lamunce Miki duk shekara ki samu zuwa mana”. Da sauri tace. “Inayi kuma, in sha Allah zan ƙara gobe ma a ɗawafin ban kwana.” Kiran da Ummeynshi tayi mushine yasa ya sallamesu, ya nufi inda su Ummeyn suke su kuma suka tafi suka shiga motocin su, zuwa makka. Da daddere bayan sunyi wanka sun ɗan huta gajiyar hanya daga Madina zuwa Makka, ne suka ɗan fita shopping Malls dake kusa dasu, suka ɗan tsitstsinto ƴan ƙananan abubuwan da ba'a rasaba. Bayan sun dawo sun gama harharda kayansu, Yah Usman yazo ya kwashi, dan za'a sasu a tawaga ta musamman ne dan jirginsu gobe da Magrib zai tashi. Nan suka zauna suna ɗan hira. wayar da Maryam keyi da Ruƙayya matar Barrister Kamal ne yasa duk sukayi shiru, saboda suna ɗan iya juyo me take cewa cike da tsananin fusata da ƙunan rai da makantar zuciya da kishi yake dirar wanda ke maida wasu mata tamkar zautattu tace. “Dan.....! By *GARKUWAR MARUBUTA* [1/3, 5:15 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 3* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin INDA RAI na kiɗine, yanzu free pages ne mukeyi, ki biya kafin a gama, 1k ne kacal zaki turo ta 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. Gareku mutan Niger 1000fc zaku biya wato jaka ɗaya kacal kenan ga number da zakuyiwa magana ku biya ta wurin Mommy +22790899076* Yauwa matan alkhairi ku matso kuji, wani sabon haɗi na musamman mai huce mana haushinmu, ya magance mana matsalarmu. Mata da yawa na koka min matsalar Basir da sanyi ya kashe musu mazanjensu, har basu iya bya msu bƙtrsu bare aje ga gamsar dasu a tarayya, wasu kan ce abin ya ƙanƙance. To kuzo da kekkyawan yaƙinin Ubangijin ya sauƙar da maganin wannan ciwon tun kafin ya sauƙi cutar. Inada haɗin na musamman na mazane ras. Hajia matsalarki tazo ƙarshe da izinin Ubangiji in kina buƙatar ƙarin bayini, kin kuma tabbatar zaki saya ne to kiyi min PC haɗin Rabin set 5k set ɗin kuma 10k akwai kuma mgni infection sadidinan shima haɗin rabi 5k set 10k.. “Dangin miji dangin shaiɗan, su Maryam manyan munafukai dangin shaidan, ashe da karuwar Yayan naki, kuka taho Makkan ban saniba?, da yake ke makirace, munafuka, baki gaya min cewa da karuwar shi ya biya manaba, ke kan ki kin sani wallahi da nasan da wata macce karuwa a cikin jerin waɗanda ya biya wa hajjin bana, wlh da bazan zoba, domin itace baƙuwar zuwa Makka, ki gaya mata cewa, ni wannan karon zuwa na bakwai kenan ina zuwa da mijina. Dan haka tun wuri kice mata ta nemi nata mijin Barrister mijin Ruƙayya ce ita ɗaya, domin Ruƙayya aka halicci Barrister ita kaɗai saboda haka ki faɗa wa wannan Karuwar banza karuwar wofi Ni Ruƙayya nafi ƙarfin haɗa miji da ita”. Ta dasa ayar mgnar cikin tsananin zafin kishin da kansa wasu mahauka tan mata iya yin komai a kan mazansu. Ita kam Aysha rumtse idanunta tayi, tare da sunkuyar da kanta ƙasa zuciyarta na wani irin suya... Garkuwa kuwa cikin mamaki take sauraren kalamanta da taci gaba da faɗa tana mamakin tsananin kishin jahilcin hauka da wasu mata keyi. Sai kuma Maryam tayi sauri katseta ta hanyar cewa. “Aunty Ruƙayya, inafa mutuntaki,Ina ganin kimarki so dan haka ki daina kirana munafuka, yadda kike matar yayana, shine ya haɗamu dangantaka, itama yayan nawa ne zai haɗamu dangantaka, kuma Aysha ba karuwa bace, ina mai kyautata nats zaton har a wurin Allah ta fiki kima, tunda ta fiki tsoronshi da bin dokokinshi domin da itace a matsayikin ba zata wulaƙantaki ba”. Wohoho ina wuta Ruƙayya ta Abka,Maryam cikin Tsananin hargowa da hayagaga tace. “Ke ƙaramar alhaƙi, ke akayan miya mecece na rantse da Allah zaki gane kin zageni, nayi miki alƙawarin sai na farraƙa tsakaninki da Yayan naki. Cikin matsanancin bugun zuciya Aysha ta runtse idanunta hawaye Masu masifar ɗumi na tsatstsafo mata. Ruƙayya kuwa cikin hargowa tamkar zata fasa Speaker wayar ta cigaba da faɗin. “Ita kuma wannan Mara aikinyi ki faɗa mata in dai Barrister take jira tayi aure, to in sha Allah a bazawararta zata mutu. Mijina nan gani nan bari awar mayya ga yaji ga albasa Amman ba daman ci, in kuma ta kuskura tayi taurin kan shigowa gidan mijina, duk abinda ya sameta tayi kuka da kanta.” Cikin mamaki Garkuwa ke cigaba da sauraron ɗaɗɗatan maganar dake fitowa daga bakin Ruƙayya tabbas wasu matan haukar kishi na shirin zautar dasu... Aysha kam tuni hawayen da take ƙoƙarin riƙe wa suka fara silalomata. Wannan dalilin nefa, yasa take tsoron aure, Shiyasa tunda suka zo makka sau uku ta yarda suka haɗu da Barrister, tunda tasan yazo da matarsa, kuma bata son ta shiga haƙƙinta, shike nan ita kuma ƙaddararta kenan?. Da sauri Garkuwa ta zare wayar a kunnen Maryam tare da katse kiran kana tace. “Yin mgna a cikin fushi kuskurene,domin duk sanda mutum yayi fushi bashi ke magana ba shaiɗan ne keyi ki bari sai kin huce, kuma ai bada kema ya kamata, tayi wannan haushinba, mijinta zata tara tayi idan tana tunanin tana da ikon hanashi Aure.” Haka dai tayi ta tausar Maryam da Aysha da tai Murmushin mai haɗe da hawaye kana tace. “Idan har aurena da Barrister alkhairi ne to ya Allah ka tabbatar in kuma ba alkhairi bane, Yah hayyu ya ƙayyum bi rahamatika astagis, ya fito min da wani mafi alkhairi a gareni”. Da Amin suka amsa baki ɗayan su. Daga nan suka kwanta kowa da tunanin da yake aransa. Barrister kuwa baima san abinda matarsa tayi ba bare yayi yunƙurin ɗaukar mataki Ƙarfe uku dai-dai suka tashi suka tafi Harami acan suka wayi gari har zuwa ƙarfe, goma lokacin da suke ɗawafin ban bakwana. Duk da yanzu dubban ɗaruruwan mahajjata sun ragu amman hakan bai hana ka'aba cikaba. Cike da kuzari da yaƙini Aysha keyin ɗawafin, tana mai nanawatawa mahaliccinmu buƙatunta. Ɗawafin takeyi tana kuma kutsawa cikin dubban al'ummar tana kara kusanto ka'aba dan so take ta jita a jikin ka'aba. Cikin yardar Allah kuma ta samu ta ƙutsa ta gefen hajarul Aswad. Wani irin matsa taji taro jama'a sunyi mata har numfashinta na kwabcewa Amman hakan bai hanata kutsawa ba, zuwa yanzu ji take kamar sawunta baya taka ƙasa, tana makalene a tsakanin kafaɗun manyan matan Chaina mutane masu kama da aljanu dan ƙarfi. Wani nannauyan ajiyan zuciya mai tafe da raunataccen kuka ta saki lokacin da taji ta jikin ka'aba. Fuskar ta ta manna da jikin Ka'aba murya na rawa ta fara jero tarin addu'o'inta da buƙatunta cikin raunatacciyar Muryar da tasa makusantatan juyowa suna kallonta. Wanda gefen damanta Ummeyn Tajj ne, gefen hagunta kuma Addawa ne sai Tajj ɗin dake tsakanin kafaɗarta data kakar tashi domin itace ta kutsa ta shiga tsakanin nasu, jin yadda ta kutsone yasa ya ɗan janye jikinshi duk da bai ga waye bane. Jin sautin kukanta da muryarta ne yasa ya juyo ya kalleta cike da mamaki. Ita kuwa Aysha cikin raunatacciyar murya da sassayan kuka take addu'o'in da yaruka uku Larabci, Hausa, fillancin. Kusan duk take haɗesu waje ɗaya. ”Yah Allah ka sauƙaƙamin ƙaddarata, ka juya min ita izuwa kekkyawa mai daɗi, Alhamdulillah Allah na gode maka ka bani rai da lfy, da damar zuwa wannan tsarkakekken wuri, Yah Allah kaine kace mu roƙeka. Ya Allah ka tabbatar min da alkhairi tsakanina da wannan bawa naka Barrister Kamal, idan har aurena dashi alkhairi ne ya Allah ka tabbatar mana dashi, ka tausashi zuciyar matarsa, ka bamu zaman lfya, ka hanani samun damar cutar da ita, itama ka hanata samun damar cutar dani. Yah Allah idan har ba alkhairi tsakanina da Barrister Allah ka sauya mana da abinda yafi alkhairi a garemu. Ka fito min da mijin aurena na alkhairi ka bayyana minshi akan alkhairi kasa mana dangana tsakanin zuƙatanmu ya Allah in dai Barrister ba alkhairi bane a gareni, ka alaƙanta wanda yake alkhairi a gareni ka kuma nuna min ranar aurena. Ka kuma sa mana haƙuri nida Barrister. Ya Allah kayi min kekkyawar rayuwa ka bani kekkyawar ƙarshe ka shafe zunubaina. Ka haskaka duhun zunubaina da hasken gafararka. Yah Allah ka raya min yarana kayi musu al'barka, ka shirya minsu bisa tafarkin gsky. Yah Allah ka bawa Mahaifiyata lfya mai ɗorewa.” Sai kuma ta kakare saboda kukan da ya taso mata daga can ƙasan zuciyarta, wanda yake son fizge numfashinta ta, da kyar ta iya jawo numfashi kana taci gaba, da jero bukatar ta, na nan gidan duniya da ƙiyama. Yayin da Ummey da Addawa da Yah Abana, duk suka zame daga wurin dan bawa wasu damar samun kusantar ka'aba, ita kuwa Aysha ji take yi tamkar wahayin buƙatunta akeyi mata Shiyasa suka ƙi ƙarewa. Tajj kuwa, tsintar kansa yayi, da shiga lamurran addu'o'inta, more especially yadda take yawan, mai-maita Allah ya bawa mahaifiyarta Dadey ta lfya ya yaye mata cutan dake damun, kawai ji yayi yana mai kwaranyowa Dadeey addu'o'in samun, lfya tare da ambaton babban sunanta Fatima kamar yadda yaji Aysha nayi. Sai kuma ya ɗaura da tayata, Addu'ar shirya ga ƴaƴanta, da take kira. Mahmood, Minat, da Khalid. Ya tsinci zuciyarsa da tayata, Addu'ar. Kana ya ɗaura dayi mata addu'ar da ta buwayi kunuwansa da ita. Samun miji na gari, da fatan in dai tsakaninta da Barrister ba alkhairi to Allah ya sauya mata. A ƙarshe suka shagala da neman rabauta na duniya da ƙiyama, da neman tsari da azabar ƙabari, da wutar jahannama, suka cike gurbin du'anin da neman jannatul Firdausi. Yayin da gaba ɗaya kwayar idanunsa ke kan ƴan yatsunta da Maryam ta watsa mata mashahurin lallen amarci. Cikin sanyin jiki, ta fara kiciniyar juyowa. Ido cikin ido sukayi dashi, lumshe idanunta tayi, sai ga hawaye shar sun kwaranyo. Kai ya jujjuya mata alamun tayi shiru, sai kuma ya zaro tattausa hankicib dinsa mai ni'imtaccen ƙanshin ya miƙa mata, tare da juyawa yayi mata alamar su fito. Ba musu ta amsa, tare da sharce hawayenta da kuka yasa idanun suka ɗan kumbura. Da hanzarin ta fara bin bayansa, duk inda ya cire ƙafarsa nan take dire tata ƙafar, domin ya zame mata Garkuwa daga cunkoson mutane ba dan shiba tana da yaƙinin wannan gabza-gabzan Matan sun turmusheta. Tafiya mai yawa sukayi, har suka fito can wajen harabar masallacin. Shi bai tsayaba ita bata daina binshi ba. Wani shago dake farkon titin da suka miƙa ɗin ya shiga, ita kuwa a bakin wurin ta tsaya, jim kaɗan da shigansa ya fito, da wata ƴar leda a hannunsa. Hannunshi yasa ya zaro, wasu tattausan safan hannun masu masifar kyau da taushi ya miƙa mata. Cikin ɗan tsura mata ido tare da tausasawa yace. “Kisa wannan, in kinyi lalle ki dai yawo haka ba safan hannun, domin junnu suna saurin shigarku ta wannan sigar, musamman ma irinki, da kike da ƙalwaya. Kuma ko a sheriya ma bai halatta ki bayyana adonki ga ko wanne Tom and Jerry ɗin ba.” Ya ƙarashe mgna da danne wani abun dake taso masa a ƙahon zuciyarsa. Amsa tayi ta sanya, kana ta amshi ledan. Daga nan suka fara tattaki, suka nufi masauƙinsu domin tsakaninsu ba nisa. Nashi ne a forko, so a bakin ya tsaya tare da kallonta cikin fuskar aminci yace. “Fatan Allah ya maidaku lfya, Allah yasa munyi Hajji Mabrooq. Idan kin koma ki gaida min Dadeey da jiki, Allah ya bata lfya mai ɗaurewa, yasa wannan ciwo nata zakkan jikine. Allah yasa kuyi farar jinya ki gaida min su Mahmood kuma kiceea Abba ina gaidashi”. Ya ilahi bazata iya hana hawayenta zuba ba, domin a duniya maiyiwa Mahaifiyarta da yaranta da Abbanta Addu'a ya gama mata komai. Kawai sai ji tayi hawaye na kwaranyo mata, kana tana amsawa da. “Amin Amin Ameeeeeeeen Ya rabbil izzati ngd matuƙa da addu'o'inka garesu, ka gaida Ummeey da Yah Abana, kace inayi musu fatan alkhairi Allah yasa ka kasance musu al'wadussaliha”. Cikin kauda kai yace. “Amin ya rabbi”. Daga nan ya wuce ciki. Ita kuwa Aysha ji tayi kamar an dasata a wurin, sai kuma ta juya da sauri jin Maryam na kiranta, nan suka shiga ciki. Alhamdulillah misalin ƙarfe. Shida kamar yadda suka zo, haka suka taso. Zuwa yanzu gaba ɗaya Mahajjata duk sun koma ƙasashensu, sai waɗanda jinya ta riƙesu, da kuma ire-iren shugabannin mahajjatan da dole, in akwai ɗan yankin su da ba lfya suke tsayuwa a kula da komai nashi. Mahajjatan Adamawa duk sun dawo cike da farin ciki da jin daɗin irin karamcin, Amirul Hajj ɗinsu yayi musu. Gashi duk kayan mutane ya dawo kan lokaci. Bayan wata ɗaya da, dawowarsu. Garkuwa ce zaune a Parlour'n Dadeey yayin da Aysha ke miƙa mata cup ɗin data zuba mata, Juice mai sanyi. Amsa tayi tare da ɗan kurɓa kana ta ajiye, tare da yiwa Dadeey sannu da jiki. Cikin yanayin alamun sauƙin jikin tace. “Yau dai ga Garkuwa a Parlour'na, tunda kuka dawo kullum sai Aysha ta bani labarinki”. Murmushin Garkuwa tayi cike da girmamawa tace. “Ayyah Dadeey ai kullum ina son zuwa Allah bai nufaba sai yau.” Murmushin Aysha tayi tare da cewa. “Maryam jiya uwar haka muna tare ai, Yah Abubakar ne ma ya maidata”. Gyara zaman Garkuwa tayi tare da cewa. “Ayyah Maryam nima last two weeks taje min, ita ce ma ke cemin Barrister baya ƙasa ko?”. Kai Aysha ta jinjina tare da kallon Dadeey dake cewa. “Uhmmmm Allah dai ya kyauta, Garkuwa lamarin Aysha akwai buƙatar addu'a kigafa irin hidimar da Barrister yayi mata, da yadda yake sonta, Amman batun aurensu ya shiririce. Ko an mishi mgna sai yace. Su bari sai gaba akwai abinda yake damunshi. Ya fito ya faɗi damuwar kuma yaƙi, abinda da kuna dawowa da kwana biyu nefa za'ayi bikin”. Cike da jimami Garkuwa tace. “Bakomai Dadeey in sha Allah, wata rana zai wuce kamar ba'ayi ba Dadeey ke dai muyi ta matta addu'a _INDA RAI to da RABO_”. Cikin danne ƙunan dake zuciyar Aysha tace. “Kayya Aunty Garkuwa ni na fara karaya da lamarina fa, hakafa duk wanda yake sona sai mgna tayi zurfi tayi nisa na gama duk shirin biki, sai abu yazo ya watse, kuma ka rasa dalili, Hakafa mukayi da Mukhtar Garkuwa naso Mukhtar har raina, Babanshi yayan Sarkin Gombe ne, lokaci ɗaya abun ya lalace, Garkuwa haukane kawai banyiba lokacin da mgnata da Mukhtar ta watse nayi kuka har na rasa hawaye, Abin takaici kuma haka ma ya faru da Yah Muhammad wani dan Kaduna, abin har ya zame min jiki yanzu kuma ga wasu ma neman sun tasoni gaba basu saniba Ni tsoro suke bani”. Abba dake shigowa ne dan duba jikin Dadeey yayi ɗan gyaran murya tare da cewa. “Ba komai Aysha in sha Allah komai zai zo da sauƙi, addu'armu gareki ba zata faɗi ƙasa banza”. Da sauri Garkuwa ta ɗan zame ƙasa tare da gaida shi, Cike da kulawa ya amsa kana ya tambayi Dadeey ya jiki, kana ya juya ya fita. Yana fita sukaci gaba da hirar, tsoron Aysha a haka har mgnar tazo kan abinda tayi a jirgi. Nan sukayi ta hirar Garkuwa na bawa Dadeey labarin yadda tayi, da yadda Taj ya taimaka daga nan sukayi ta hirarsa. Cikin kwaɓe fuska tace. “Shifa da gaske gani yake aljanu gareni”. Cikin dariya Garkuwa tace. “Yoh ai koni lokacin kallon mai aljanu nayi miki.” Tana gyara zamanta tace. “Ai baki sani ba, rana ita yau iwar haka, kawai sai naga, kira naso in gane number Amman sai na sha'afa. Ina ɗagawa naji shine!”. Da sauri Garkuwa tace. “Ke haba dai dan Allah”. Tana gyara wuyan rigarta tace. “Wallahi kuwa, wai ya kirani yaji ya jikin Dadeey har na bata waya suka gaisa dashi, harda Abba ma, sun gaisa”. Da sauri tace. “A'a Aysha ko dai? Ko dai?”. Da sauri cike da gsky da gsky da ya ƙini Aysha tace. “Yah salam ba wannan mgnar wlh, kin dai san ni nafi son babban mutum”. Kai Garkuwa ta jinjina domin tasan yes Aysha tafi son babban mutum irin mai mata da yara haka dai. Ganin la'asar tayi ne yasa suka miƙe sukayi sallan la'asar. Bayan sun isar ne, Garkuwa ta gyara zamanta tare da cewa Aysha. Yayan ta Usman nefa ya aikota cewa yana sonta. So sanin su waye su yasa tace, Allah ya tabbatar musu da alkhairi duk da Usman saurayine Amman tasan ya girmeta nesa ba kusa ba, duk da dai tasan bata da ra'ayin auren saurayi Amman ta nemi zaɓin Allah, daga ranar Usman ya shiga cikin jerin masoyanta. Yau watansu biyu cib da dawowa, konce take a ɗakinta, tunda tayi sallan azahar bacci yayi gaba da ita cikin, baccin ta fara jiyo ringing ɗin wayarta, a hankali ta ɗan motsa tare da buɗe idanunta ta kalli Fuskar wayar, number Ethiopia ce kana ga sunan Tajj yana yawo a sama ne yasa ta ɗauka tare da karawa a kunne. A hankali ta kuma lunshe idanunta saboda jin sassayan sautin muryarsa daya ratsa kunnuwanta, cikin yanayin bacci tace. “Assalamu alaikum Tajjj”. Sai kuma tayi kasake jin yana cewa. “Wa'alaikissala Afwan Ishmah bacci kikeyi ko na tadaki?”. Kai ta ɗan jujjuya tare da cewa. “Gwarama daka tada ni, ai lokacin salla ya ƙarato”. Numfashi mai sanyi ya fesar tare da cewa. “Toh yanzu dai ya jikin Dadeey”. Murya a narke tace. “Alhamdulillah jiki da sauki kwanan kuma ya sake tashi”. “Allah ya ƙara mata lfy, ya Abba dasu Khalid suna lfya ko?”. Cikin jin daɗin kulawarsa ga iyayenta da yaranta tace. “Lfy Lau Alhamdulillah, Yah Ummey da Yah Abana”. Cikin sanyi yace. “Suna lfya. ki bawa Dadeey waya mu gaisa”. Toh tace tare da kaiwa Dadeey wayar suka gaisa, kana tace. “Ba kaƙi ka haɗani da Ummeey ba, sai Addawa sarkin rigima”. A hankali yace. “Kiyi sallan zan kiraki”. Toh kawai tace kana ta katse kiran. Bayan ta idar da salla kuwa ya kirata sukayi ta, hira wanda mafi akasarin akan abinda tai a cikin jirgine. Ya ƙara da cewa. “Yau ne na samo wata passinger daga Jordan zuwa Palastine itama tai tayin yadda kikayi, sai ta tuna min da ke, tunda na fara aikin ku biyu ne, naga kunyi haka”. Cikin murmushin mai haɗe da kunya tace. “Wai kai baka mantuwa ne”. Kai ya ɗan rausayar tare da cewa. “A dai naki kam bazan manceba”. Murmushi tayi tare da cewa. “Kwanan ma da Garkuwa tazo muna hirar mukayi ta dariya”. Cikin kulawa yace. “Me tazo yi?”. Kamar a fizge taji mgna ta fito bakinta. “Wai tazo ta gaya min wai yayanta Usman na sona, yana nan da fuskarsa kamar mace ba saje”. Sai kuma tayi saurin rufe bakinta. Shi kuwa Tajj a hankali ya ɗaura hannunsa bisa tattausar fuskarsa, da mafi akasarin ranaku sai ya yaɗe sashensa da gemun. Cikin nazari yace. “Toh ina Barrister abin ya watse ne?”. A hankali tace. “Eh”. Shiru sukayi baki ɗayansu, fahimtar kamar ya fama mata mikin rantane ya sashi cewa. “Toh ke me ruwanki da rashin sajen na miji ai ba saje zaki auraba ko?”. Cikin yin ƙasa da murya tace. “Ai fuskar namiji in ba saje da gemu, bata da banbanci da fuskar mace, ni bana son namiji ba saje”. Kai ya jinjina, tare da cewa. “Ok yanzu dai bawa Dadeey waya inyi mata sallama”. Miƙewa tayi ta shiga Parlour'n Dadeey bisa sallaya ta sameta a zaune, miƙa mata wayar tayi tare da cewa. “Tajj ne wai zai miki sallama”. Amsa tayi, ita kuma Aysha sai ta zauna a gefe Dadeey kuwa gyara riƙon wayar tayi jin, Tajj na cewa. “Dadeey ya jikin da sauƙi sosai ko”. Yayi mgnar cikin gyara fillancinsa na Ethiopia yadda zata gane sosai. “Eh Alhamdulillah Tajuddeen jiki da sauƙi sosai ma”. Cikin jin daɗi yace. “Masha Allah haka nake son ji, Allah ya ƙara lfy Dadeey sai kina ɗan motsa jikin”. Kai ta gyaɗa kana yana mai ci gaba da bata shawarwari irin nasu na Doctors. Daga bisani sukayi sallama. A hankali rayuwa taci gaba da juyawa, yanayi na sauyawa. Kwanaki na tafiya makkoni na shudewa watanni na mirginawa izuwa shekaru. Bayan tsawon shekaru huɗu kenan. Abubuwa da dama sun faru cikin shekarun nan. More especially tsakanin Aysha da Tajj, wanda suka gina wata tsabtacecciyar amintakar, dake bisa wani ɓigiggiren, da su kansu basu san na menene ba, sun zama aminai na musamman wanda duk motsin ɗaya, ɗaya na sani. Sunyi wata iriyar shaƙuwa mai haɗe zuƙata tasa su bawa juna dukkan yarda, Tajj bai taɓa wani abokiba a duniya sama, da marigayi pilot Irfan Imran wanda aka kashe a faɗar tsakanin Palastine da Isra'ila. Dashi da iyayensa baki daya sai ƙanwarsa Laylah yar shekaru sha biyu, wacce Taj ya ɗaukota riƙonta ya dawo gareshi a Ethiopia a gaban Ummeeyshi. A rayuwar Taj ba abinda Aysha bata saniba, haka shima, hatta denginta ba wanda bai sanshi ba, zuwa yanzu Abba da Dadeey kam jinsa suke tamkar ɗansu, duk da bai taɓa zuwa sun ganshi ido da idoba. Aysha kuwa Jarrabawar Aure har gobe, tafiyar bata sauya zaniba. Shaƙuwarta da Garkuwa kuwa abin ya wuce ƙawance ya zama ƴan uwantaka babu abinda ke ɗan sata faranci gami da ɗebe mata kewa kamar karanta littattafan Garkuwa domin a littafinta take samun Darussan rayuwa Ilmantar, Faɗa karawa,kana da Nishaɗantarwa idan tana karanta littafin ji take tamkar azahiri abubuwan ke faruwa... Maryam ƙanwar Barrister kuwa, Yah Abubakar ɗinta ya aureta har su haihu, Barrister da kanshi zumunci sukeyi sosai dan yana yawan zuwa duba jikin Dadeey da yake ɗan yawan matsa mata ga kuma ƙarin zumuncin da ƴar uwarsa na gidan. Hakama Mukhtar sosai suke zumunci haka Yah Usman auren ne dai Allah bai sauƙar da shiba. Shaƙuwarsu da Taj ya wuce dukkan zaton ma zato da nazarin mai nazari, domin halattacciyar shaƙuwace wacce babu saɓon Allah ko kuma gurɓacewa wanda mafi yawan Samari,Ƴan mata da kuma Zaurawa keyi Abota ce da aka gina ta saboda Allah mai cike da sanya zukata nutsuwa. Zuwa yanzu kuwa, karatuttukan Taj da muryarsa sun zaga duniyar social media, Musamman,Tik-tok,Instergram, Facebook, WhatsApp da sauran Man hajojin sada zumunta domin salon Muryasa tana da maganaɗisu na musamman ga zukatan musulmai koda kuwa baka san mai ake faɗa ba Muryarsa nada wani irin ƙwarjini mai tafiya da hankalin mutum da samar da cikakkiyar nitsuwa da cika zuciya da shauƙin ƙaunar jin karatun ƙur'ani. Yau ta kasance ranar jumma'a ce. Ƙarfe ɗaya dai-dai jirginsu ya sauƙa a Addis Ababa bole intranational Airport. Jim kaɗan da sauƙarsu, bayan an gama gwada dukkan lafiyarsa. Da sassarfa ya fito ya shiga motar da tuni aka tanadar masa da driver'nsa da tafiya gida. Yana shiga motar yacewa driver. “Dan Allah kayi gudu na gasken-gaske domin so nake, in samu jami'in sallan jumma'a a matsalacin. Grand Anwar Mosque nadan Ya Abana na jin daɗi in jashi jam'i”. Ya ƙare maganar yana kallon Driver da sam baya sauri yadda yakeso, kuna shi sauri yake domin so yake ya samu ya kasance a sahun forko bayan Yah Abana domin shine yake limancin masallacin. Wayarshi ya zaro tare da kiran Aysha tana ringing kuma bata ɗagaba. Tsaki mai sauti yaja, domin badon sanin cewa, dokar sune pilot bazasu jan motaba, saboda zasuyi gudu na fitan hankali kasan cewar sun saba da gudun jirgi, badan haka ba da tuni ya amshi tuƙin nan. Damin cike yake da begen ganin shi cikin ahlinsa, dan yanzu a ƙalla wata uku kenan bai zo Ethiopia ba, kuma duk saboda Meymey ce. Sake kiran Aysha yayi a karo na uku, numfashi mai sanyi ya fesar jin ta ɗaga. Cikin aminci yarda shaƙuwa mai zurfi yace. “Ina kika shiga inata kiranki bakya ɗagawa??”. “Ina shafawa Dadeey maganine”. Tayi mgnar tana nazartar muryarsa sai kuma tace. “Kamar kana hanya ko?”. Cikin sauƙe numfashi yace. “Eh shine na kiraki ai muyi tafiyar tare, yanzu na sauƙa cikin Ethiopia”. Tana gyara kwanciyarta tace. “To muje in rakaka”. Hannunsa yasa yana shafa tattausan sajensa mai masifar sulɓi da sheƙi, kana yace. “So nake in samu jami'in sallan bayan Yah Abana, kuma sam driver nan baya sauri, ji nake zanfa karɓi tuƙin”. Da sauri ta ɗan ware manya idanunta alamar tsoro sai kuma ta langwaɓar da kai cikin sanyi tace. “Please kada ka amshi tuƙin nan, bana so”. Cikin zu bawa tarin motocin da ya hango a gabansu bila adadin idanu yace. “Toh yadda kika ce za'ayi”. Ya ƙare maganar yana leƙa gefe da gefen hanyar ya gane, sun iso Ousman Ibn Affan Tero Masjid ne, kuma shima masallacin jumma'a ne, duk da ya hana subi kan manyan titunan ne saboda sanin, zasu samu an rurrufe hanyoyin yasa yacewa driver subi tsakiyar anguwannin, cab yama mance da wannan masallacin. Bisa dukkan alamu kuma ana gab da tada iƙamane, gashi hanyar an rufesu tako ina. “Yah Salam”. Shine abinda yace a dai-dai lokacin da yaga ta bayan nasuma motoci sunfi takwas. Cikin sanyi yace. “Dole inyi salla anan fa Ishmah”. Cikin son amintar mishi da hakan a zuciyarsa tace. “Eh ba matsala ai Tajj kayi a wurin, ana idarwa sai ka tafi, ka samu ayi liyafar family na yau da kai, tunda kana garin”. Kai ya jinjina tare da cewa. “Toh in kashe ko in bari, zakiji sautin sallanmu”. Cikin yanayin shaƙuwa tace. “Bari inji karatun limamin ko zai samu rabin maki naka”. Murmushi yayi sai kuma ya ɗan jin-jina kai kana yace. “To an gama”. Sai kuma ya kalli Dottijon driver nashi tare da juya harshe zuwa Ethiopia's language *Amharic* yace. “Abu Hashim mu tsaya muyi salla a nan, kana da al'wala ko?”. Cikin alamun tarin mutunta juna Abu Hashim ɗin yace. “Na'am”. Daga nan suka fara kutsawa cikin masallacin. Kasancewar babban masallacine kuma a ɗan luƙu yake a tsakiyar anguwannin Shiyasa baya irin cika da batsewar nan. Cikin hikima suka samu suka shiga a har ciki, cikinma sahun farko saboda shiɗin ya kasance mutum sanne a duniya ma baki ɗaya bare kuma ƙasarsa ta haihuwa, duk wanda aka cewa Sheykh Afif Muhammad Taj dole zai sanshi, domin Ethiopia baki ɗaya tana alfaharin kasancewarsa ɗan ƙasar tasu. Ahankali ya zuro ƙafarsa daga cikin mota wanda ke sanye cikin wani sau ciki baƙi mai masifar kyau da sheƙi yayin da jikinsa ke sanya cikin wani yadi mai sulɓi da taushi Army Color daya haska fatarsa yayin daya ɗaura Farin Suit asama Kansa na sanye da hula yayin da kwantaccen sajensa ya sake ƙawata kyawun fuskarsa cikin sassarfa ya ƙarasa shiga harabar masallacin. Suna isa ana data iƙama. Bayan an idar da salla an sallame, kowa yayi addu'o'insa da tasbihansa. Shima haka Taj, a hankali ya zaro wayarshi tare da karawa a kunne murya a sanyaye yace. “Kinji mun idarko yanzu zamu fita”. Murmushi mai ɗan sauti tayi tare da cewa. “Naji karatun limamin Amman bai kai naka daɗiba fa.” Yunƙura yayi da niyar tashi sai kuma yaji ana sanarwar akwai ɗaurin auren da za'ayi yanzu ana roƙon mutanen su ɗan dakata. A hankali ya koma ya zauna bayan Abu Hashim. Kana yaci gaba da mgn da Aysha. Da sauri ya ɗago kanshi ya kalli mutumin dake sanarwar cewa. “Dangin angofa sun fasa auren bisa wani dalili mai girma da kuma tuburewar ango na cewa ya fasa aure. Innalillahi wa innalillahi rajiun. Shine abinda wani kamilin dottijon mai cikar kamala ya fara nanata wa, yayin da lokaci ɗaya jikinsa ya ɗauki kerma tuni idanunsa suyi jazir. Da sauri ya kuma kalli tawagar dangin angon da suka ɗauki, kayan ɗaurin aurensu irin Goro, Dabino, cingam, da dai sauransu, sun juya sun fara fita. Da sauri ya kuma maida ganinsa kan dottijon nan da yaga ya fara rarrafawa, ya isa gaba Abu Hashim, wanda dai-dai wurin dangin Angon suke, cikin wata iriyar matsoracciyar murya mai nuna dottijon bashi da ƙoshin lfyma, ga kuma gigita, hawaye na kwaranya a idanunsa ya riƙo sawu, ɗaya daga cikin dangin angon murya na rawa cike da raunin neman alfarma yace. “Innalillahi wa innalillahi rajiun, dan Allah da son Manzon mu Muhammad (S.A.W) ku rufa min asiri. Ayi auren nan wlh bani da wani buri da fargaba da ya wuce in aurar Adaya kafin barina duniya. Nayi muku magiya da girman Allah, ku bari ayi auren nan”. Sai kuma ya fashe da zazzafan kuka. Wanda har Aysha najin duk abinda ke faruwa, cikin sanyi tace. “Allah tsarki, meyasa zasu fasa, dan Allah Taj ka tayashi basu haƙuri ayi auren nan”. Ta ƙare maganar da iya gskyarta da kuma sanin irin ciwon da mahaifin yarinyar da ita kanta yarinyar zataji, saboda ita tasan zafin dake cikin fasa aure, in ba mai ƙarfin zuciyaba, sai ta buga ya mutu. Shar-shar taji hawaye na kwaranyo mata, lokacin da taji sautin muryar dottijon nan ya saki raunatacce kuka yana cewa. “Ma'aruf ka gani ko, yan zuma a karo na uku kenan ɗaurin auren Adaya na watsewa. Ma'aruf zuciyata zata buga saboda matsalar Adaya, Zatayi ajalina, Ma'aruf ka bisu ka roƙesu da girman zatin Allah su cika min burina kafin wa'adina ya cika, nasan idan na mutu nabar Adaya batayi aureba, ruhina bazai samu salamaba”. Ya ƙare maganar da kife kanshi a jikin filar masallacin ya saki maraitaccen kuka, wanda aka kira da Ma'aruf ɗinma kuka yaleyi. Tajj kuwa lip inshi na kasa ya jiza da ƙarfi, sai yake misalta da ace Yah Abananshi ne ke kuka hakan ya zaiji a cikin ransa, Yasan ji zaiyi kamar zai suma, ya kuma tabbatar sai yayi duk yadda zai yi ya tsaida mishi hawayen nan. Sai kuma ya maida hankalishi kan Ishmah dake mgna cikin tausayawa. “Dan Allah Taj ka taimakawa tsohon nan, Please ka tsayar mai da zuban hawayensa”. Cikin sanyi murya yace. “Please Ishmah kada kiyi kuka, kin san cewa kukanki na ƙona min zuciya ko, gaya min wanne irin taimako zan mishi”. Da sauri tace. “Ka tayashi basu haƙuri ayi auren!”. Cikin jin kukanta na hautsuna mishi lissafi yace. “Ai har sun riga da sun tafi”. Da sauri ya zazzaro idanunsa jin abinda tace, murya a kaɗe yace. “eyeh hello mai kikace”. Cikin rauni da kuma iya gskyarta kana da shesh-sheƙan kuka mai cike da rauni tace. “Tajj ka aureta!!!”. Da ƙarfi ya koma ya jingina da jikin gini, sai kuma ya kalli Dottijon nan da yake kuka harda majina yana bin. mutane yana kama hannunsu yana cewa. “Dan Allah ka auri ƴata Adaya na baka ita.” Mafi akasari sai su kauda kai. A haka har ya iso gaba Taj. Riƙe hannayensa yayi duka biyu, murya na rawa yace. “Dan Allah dan soyayyarka da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, dan tsarkin Alkur'ani da yake kanka a haddace, da kimar iyayenka Afif ka auri ƴata Adaya na baka ita duniya da ƙiyima ka aureta ka amintar da ita domin irin kane mijin daya dace da ita.” Jin kalamansa ne yasa jikinsa wani irin saƙewa yayi luƙus sai kawai ya zauna dirshan. Kana a sashin Ishmah kuwa cikin taya dottijon nan magiya tace. “Taj! Taj!! Taj!!!”. Sai a kira na ukun ne ya iya furta. “Uhmmmmm”. Cikin tausasa lafazi murya na rawa tace. “Dan Allah dan Annabi da darajar Yah Abana da kuma ƙaunarka da Ummey da Amincinmu, da gskyar abotarmu, da mutuntakarmu, ka aureta ka tsaida hawayen dottijon nan”. Ya ilahi ya mujibat da'awati, yah hayyu ya ƙayyum bi rahamatika astagis, innalillahi wa innalillahi rajiun”. Sune iya ababen da yake iya furtawa a bakinsa sai kuma yayi saurin cewa. “Shiru Ishmah na amince zanyi wannan taimakon saboda Allah da Manzonsa da ke”. Yayi mgnar da Yaren Hausa da zama shi da itane yasa ya fara iyawa kaɗan kaɗan. Kana yayi Hausanne saboda yasan da wuya a samu wanda zai gane a cikin mutanen wurin, Amman in fillancin Ethiopia yayi wasu zasu iya ganewa. Sai kuma ya saki wani irin sassayan numfashi tare da kallon kamilin dottijon nan mai cike da kima kamala da rauni da yake ta zubda hawayen da magiya. “Ka taimakeni ka auri Adaya Afif kayi min wannan taimakon, in kayi min haka ka gama min komai a aduniya, Dan Allah ka auri Adaya”. Wayarshi ya zaro tare da rubutawa Abu Hashim text message ya tura mishi. Da sauri Abu Hashim ya zaro wareshi jin alamun saƙo ya shigo. Sai kuma ya jinjina kanshi tare da zaro kuɗin daga aljihunsa, kana ya irgasu, dubu 1,22000 ne kuɗinsu na can. Da sauri ya miƙe ya nufi mall da ke cikin harabar masallacin. Dabino da sweets ya seyo katon bibbiyu Kana ya dawo da sassarfa ya zauna gefen. Dottijon da har yanzu yake riƙe da Tajj yanayi mishi magiya hawaye na ɗiga bisa tafukan hannun Taj ɗin. Gyara zama Abu Hashim yayi tare fuskar Dottijon nan da yake gab da sumewa, cikin yarensu Aromo yace. “Ni Oumar Ibarahim ina nemawa, ɗana Tajuddeen auren yarka Adaya ga sadaki mu, naira dubu 100”. Wani irin dogon numfashi Dottijon yaja tare da juyawa ya fuskanci alƙibla yayi sujudushukur kana ya juyo ya kalli Taj tare da cewa. “Alhamdulillah kayi haƙuri kaga na takuraka duk da na fahimci baka so. Toh Alhamdulillah gashi mun samu wani zai aurawa ɗansa ita”. Yayi mgnar tare da juyowa ya fuskanci Abu Hashim da ba wanda ya sanshi a cikin masallacin. Ma'aruf ne ya kalleshi cike da son gano wani aibu ko naƙasu tare dashi. Amma. Ina babu saboda Abu Hashim yana samu albashi mai gwaɓi a hannun Taj Shiyasa in kan ganshi bazaka gane sana'arsa ba, to driving ɗinma da sai Taj na garine haka yasa a wadace yace gashi mutun ne shi kamili mai haiba. Kuma in kaga yanayisa dole yana da ɗa kamar Tajj. Nan take kuwa a wurin aka ɗaurin auren. Adaya da T..... *Shi wannan littafin salon sa na dabanne ni kaina yana tsumani, ki biya koyi karatu cikin aminci 1k ne kacal fa 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276, ku kuma mutane Niger 1000fc ne jaka ɗaya kacal kenan +22790899076 Zaku biya ta wurin Mommy* By *GARKUWAR MARUBUTA* [1/4, 12:58 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 4* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin INDA RAI na kiɗine yanzu free pages ne mukeyi ku biya in saku a group, ku karanta cikin aminci ba haƙƙin kowa bisa kanku, 1k ne kacal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. Gareku mutanen Niger 1000fc ne zaku biya jaka ɗaya kenan ga number wacce zakuyiwa magana +22790899076 Please a mutunta shekarunta babbar macece.* *Haɗin amarya budurwa mai ƙarancin shekaru da mai matsakaicin shekaru da kuma mai ɗan yawan shekaru, kana haɗin amarya bazawarar da take da ragowar ƙuruciya, da mai matsakaicin shekaru da wacce shekaru sun ɗan ja, hadi dai-dai da halittarki ƴar uwata, ƙawata, ƙanwata, ƴata, ƴaƴata, kai harma da ke kakata, akwaisu masu maida tsohuwa yarinya, duk mutuwa da sakewar fatar nan zata tattare da tsuke ta katse ta rayu da ni'imtaccen yayyafin gyaran zaman aure. To wai ke mai jego ina kike akwaisu fa naku haɗin, in ma yawan* *haihuwa yasa wurin ya sake ya kuma ƙafe, barden goyo ko ɗanyen goyo, akwai haɗinku Zaki min bayanin me matsalarki! Sakewa ne? Rashin ni'ima ne? Rashin feeling ne, ko rashin kuzari ne Duk fa akwai haɗinshi haɗin uwar gida ko tsakar gida duk akwai, set ɗin na hawa hawane, duk ƙanƙantar kuɗin Customers na baya zuwa ya koma baya, ƙananan set ɗin daga 40k ne zuwa ƙasa 35k 30k 25k 20k 15k ƙaramin haɗina ɗan autan 12k sai haɗin robor ƙasaitacciyar macen 5k. akwai manyan set ɗin daga 50k 60k 70k 80k 90k sai sha kunɗum ɗin 100k. Sai maganin infection set 10k rabin 5k Maliƙi 5k daɗi har maɗiga 5k akwai haɗin kazar 12k akwai zabuwar 20k in dai a shirye kike ga 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, ta wannan number zaki turo min shaidar biyanki 08069423567 itace ta Customers ɗina na kayan ɗa'a* Tajuddeen Muhammad Tajuddeen, (Afif) kenan saboda sunan kankanshine yaci. Tajuddeen Shiyasa akayi masa laƙani da Afif. Sai Afif ɗin kuma ya danne Tajuddeen ɗin. Shiya sai na kusa da shine kaɗai suka san hakan. Hakan yasa ko mutum ɗaya bai gane cewa dashi Afif aka ɗaura aren Adaya ba. Shi kuwa Taj ana gama ɗaura auren bisa sunan da ƙa'idar addinin musulunci. Yaja wani ɗimautaccen numfashi tare da zurawa, Abu Hashim idanu, ganin Dottijon nan ya jawo hannunshi tare da cewa. “Bismillah ko Malam Ousman muje, kaga gidana, yana nan gefen masallacin, muje in danƙa maka hannun Adaya ka kaiwa ɗanka.” Da sauri Abu Hashim ya juyo ya kalli Taj domin kalaman dottijon sun zo musu a bazata. Shi kuwa Taj wayarshi da yayi mishi text message dashi ɗazu, ya kumayi mishi wani text ɗin. Da sauri Abu Hashim ya zaro wayatarshi daga aljihu, tare da duba saƙon. Murmushi ya ɗanyi tare da miƙewa tsaye tare da fara gaisawa da mutanen dake ta miƙa mishi hannun daga bisani suka fita. Taj kuwa yunƙura yayi tare da tattaro ragwar ɗan kuzarinsa ya miƙe tsaye tare da binsu a baya, tafiya yake yi tamkar babu laka a jikinsu, tarin ƙalubalen dake gabansa a lamarin yake hasasowa yadda zai fuskanci mahaifinsa yayi mishi wannan bayani mai kama da tatsuniya ko mafarki, ko hikayar cikakkun marubuta mai cike da sarƙaƙiya. Numfashi mai nauyi ya sauƙe tare da rumtse idanunsa, ya sani ko Ummeynshi bazai iya fuskanta ido da ido wai yace mata, yayiwa kanshi aure ba, bare kuma Yah Abananshi da ya san halinshi farin sani, baya ɗaukan wargi, yatsunsa biyu yasa ya sharce zufan dake tsatstsapa mishi bisa goshinsa. A hankali ya jingina jikin motarsu, tare da rumtse idanunsa, ya sani Ko babban yayansu, Hafiz bai isa yayi aure mahaifinsu bai saniba, wanda shima yana da yaran da sun kusa aurema bare shi, ya Salam shine abinda ya furta a tsakanin lips inshi, runtse idanunsa yayi tare daci gaba da mgnar zuci dake tabbatar mai da cewa Ishmah na juya tunaninshi da kwanyarsa ta yadda baya iya ƙin yin duk wani abinda zai sata farin ciki, Allah ya sani ji yake rayuwarsa bazata samu cikakkiyar nasarar in har bai sata farin ciki ba. Ido ya zubawa Abu Hashim da Dottijon nan da wasu mutane da basasu, gaza huduba, sunka nufi wani gate, da yake fuskantar harabar masallacin. Lunshe idanun yayi kana ya buɗesu, ganin sun shiga wannan gidan, wanda bisa dukkan alamun nanne gidansu Adaya. A wani matsakaicin Falo suka zauna, Cikin hikima Abu Hashim ya gyara zama da bin mgnar da Taj ya rubuta mushi, ya kalli Dottijon tare da cewa. “Toh Alhamdulillah yanzu dai naga gidan, zan koma nawa gidan kuma in shaidawa mahaifiyar yaron da shi kanshi yaron, dan a kimtsa inda zata zauna a kuma shirya mata, tarbar da ta dace.” Cikin jin daɗi Dottijon yace. “Kai Alhamdulillah naji daɗin jin haka kuwa, amman yaushe za'azo ɗaukarta”. Cikin sauri yace. “In sha Allah nan kusa, mijinta da kanshi zai zo ya ɗauke, tunda naga gida ai komai yazo da sauƙi”. Cikin gamsuwa dottijon da sauran duk suke gyaɗa kai domin haka nan, sukeji sun aminta dashi”. Shi kuwa dottijon gyara zama yayi tare da cewa. “Toh muna nan muna tsumayinku”. Daga nan suka ɗan tattauna. Daga bisani suka fito. Taj dake zaune cikin motar tasu, yana mai ƙara tsare gidan su Adayan da idanun yana kallon lungu da saƙo na sashin wurin, Rakiya sukayi wa Abu Hashim har gindin motar, wanda basu ga Taj a cikiba kasancewar glass ɗin motar tintek ce. Ma'aruf ne da kanshi ya buɗe mushi marfin gaba, da sauri ya shiga tare da cewa. “Toh sai kunjini”. Fatan sauƙa lfy sukayi mushi. Tare da raka motar tashi da idanun, har ya ɓacewa ganinsu kana suka koma cikin gida. Taj kuwa har yanzu wayarsa, na maƙele a kafaɗarsa, domin bai katse kiransa da Ishmah ba. “Uhmmmmm”. Ya sauƙe numfashi, jin tana cewa. “Taj kayi mgna mana, Please kayi mgna menene matsalarka?”. Cikin ƙarfin hali ya buɗa lips inshi a hankali, kana ya haɗesu tare da rumtse idanunsa murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Ishmah! Meke faruwa dani ne? Wai me nayi ne? Me zan cewa Ummeyna, Ishmah Yah Abana bazai ɗauki wannan wargin bafa”. Cikin ɗaurewar kai ita kanta take nazartar kalamansa. Wanda kamata yayi suyi wannan tunanin kafin mai abkuwa ta abku, domin wannan ya zama tamkar hikaya, ko mafarki mara tushe cike da kullewan kai tace. “In sha Allah, komai zai zo da sauki Malam zai fahumceka, Ummeey zata zame maka hasken da zai gamsar da malam, Please ka kwantar da hankalin ka kaji Bestie”. Ta kiranshi da sunan da tasan, in ta gaya mishi yake rufeta da faɗa dan ya tsami sunan, ita kuwa so take yayi faɗan ko zaiji sassaucin damuwar da ta fahimci tayi silar shigarsa ciki, domin tafi kowa sanin zurfin cikinsa. Shi kuwa Taj cikin rumtse idanunsa yace. “Sai anji ma”. Yana faɗin haka ya katse kiran. Ido ta zubawa wayar kamar ta samu, abin kallo a jiki. Shi kuwa Taj murya a ɗimauce yace. “Abu Hashim gida zamu wuce”. Yayi mgnar da yaƙinin yasan zuwa yanzu Mahaifinsa da yayunsa maza, duk sun koma gida. Cikin girmamawa Abu Hashim ya amsa mishi, kana ya ɗauki hanyar gida. Cikin kulawa Abu Hashim yayi parking a farfarjiyar wani, ƙaton gida da yafi kama da fada, Sai dai ba fadan bane, kawai tsarin gininne alfarmar wanda kallo ɗaya zakayiwa gidan ka gane cewa. Babban gidane na babban mutum mai tarin zuriya, ƴaƴa da jikoki. Da sauri Abu Hashim ɗin ya fito tare da buɗewa Taj marfin motar. Cikin mutuwar jiki ya ziro ƙafarsa waje, ba tare da ya miƙe tsayeba, ya kamo hannun Abu Hashim, wanda hakan yasa ya sunkuyo, cikin sanyi murya yace. “Afwan Abu Hashim, duk da nasan kai mutum ne mai amana da riƙe sirri. Amman zan kuma roƙonka da girman zatin Allah wannan al'amari ya zama sirri dagani sai kai, sai Allah, Please kada ka gayawa kowa, har sai na samu mafita”. Cikin bayyana cikar amana da sirrantaka Abu Hashim yace. “Nayi maka al'ƙwarin duk duniya babu maijin wannan mgnar a bakina, in sha Allah”. Cikin gamsuwa ya miƙe tsaye, tare da nufar asalin cikin gidan. Cike da girmamawa Mai aikata gidan duk suka nufo garesu. Driver Malam ne ya amshi jakar dake hannun Abu Hashim tare da cewa Taj. “Barka da isowa Abban Abba”. Cikin ƙirƙiro murmushi dole ya kallesu tare da amsa gaisuwar da suke masa. Tafiya mai ɗan tsawo sukayi kana suka, isa tsakiyar gidan, Da gefen hagu da dama suke ɗauke da tsala-tsalan part guda bibbiyu komai nasu, iri ɗaya wanda 3-3 bedroom ne sai 2 Parlour, and dinning area, sai kitchen, kana da sito, Sai kuma wani babban part da yake tsakiyarsu yana fuskantar alƙibla wanda shima 3 bedroom ne, sai kuma Parlour manya guda uku, sai ta bayan shi dake shimfi da wani ni'imtaccen gardin wanda yake ɗauke da nau'wukan itatuwan kala daban da ban, sai kuma wani ƙaton Parlour da yafi kama da holl wanda aka ƙawatashi da kayan ƙawa na alfarmar kuma shine falon forko. Sai kuma can bakin gate da ɗauke da BQ babba 2 bedroom sai babban falo, sai kuma sashin ma'aikata. Suna isa tsakiyar harabar cikin gidan wasu ƴan dugui-dugui ɗin yara suka fito daga part ɗin dake kusa dashi wanda, suke gab da bakin ƙofar sai, cikin tsananin jin daɗi babbar cikinsu da bazata gaza shekaru takwas ba, ta buɗe murya da iyakar ƙarfinta tare da faɗin. “Oyoyo Uncle Afif”. Ta ƙarashe kiran sunansa da masifar ƙarfi tare da nufarsa da gudu. Cikin abinda bai gaza one minute ba, sai ga yara na fitowa ta ko wanne part a ƙalla sun kusan goma, gaba ɗaya sun ruɗa gidan da kiraye-karayen sunan. “Oyoyo Uncle Afif.” Cikin jin farin cikin ganin yaran ya ɗan rusuna ƙasa, tare da ware hannayensa. Kamar tattabaru haka duk sukazo sukayi mushi zobe, Yarane masu shiga rai da samar da farin ciki. Murmushi Ummeey dake cikin kitchen dinta ita da babbar ƴarta Maryam. Cikin tsananin jin daɗi tace. “Alhamdulillah Babana ya iso”. Cikin Murmushin Maryam tace. “Bari in tafi nasan wurin Malam zai wuce. Rashida ce wacce ita ke bin maryam ta shigo yayin da Halima ke biye da ita a baya, wacce ita Taj ke bi. Cikin murmushi da bayyanenne jin daɗi tace. “Ummeyy albishir. Cikin murmushi tace. “Naji ai yadda ƴaƴanku suka cika gidan da ihun Uncle Afif ya iso”. Da sauri Zakeeya ƙanwar Taj mai binshi duk da tsakaninsu kusan shekaru goma ne, kana itace ƴar autar Ummeey, shigo kitchen ɗin fridge ta buɗe tare da ɗaukan Apple, Grapes, cherry, strawberry. ta ɗaurayesu tare da goran ruwa mai sanyi tana fita tace. “Ummeey Uncle Afif fa ya iso”. Da yake itama haka take kiranshi. Kusan a tare ita dasu Rashida duk suka fito. Shi kuwa Taj tuni ya ya shiga Parlour Malam tare da zugan ƴaƴan yayunshi da kuma ƙannensa. Suna shiga Parlour, Malam ya saki wani irin murmushin dake bayyana tsananin so da ƙaunar da yake yiwa Taj ɗin. Shi kuwa Taj cikin sauri ya dire wata yar kekkyawar baby da bazata gaza shara ɗaya ba, ɗiyar Yah Hafiz ce. Yana ajiyeta, kuwa ta saki ihu, haka yasa yayi saurin ɗaukarta, Tare da ruggume Yah Hafiz ɗin. Wanda shine babban ƙab gidan nasu, sai Kuma Yah Sulaiman da Yah Yusuf suka ruggumeshi a tare. Suna mai ɗan bubbuga kafa ɗarsa, tare da sumbatar gefen kuncinsa. Shi kuwa murmushi dake bayyana irin tsananin yadda yake son ƴan uwan nasa yayi tare, da juyowa ya nufi Malam. Hannun Mahaifin nasu ya buɗe mishi alamun yazo. Da sassarfa ya ƙarasa gabanshi tare da durƙusawa bisa guiwowinshi. Haka ya basu damar ruggume juna, hannunshi yasa ya tallabo fuskantar Taj da farin cikin ganinsu yasa ya fara mance kitimurmurar daya haɗawa kanshi. Sassayan sumbata ya direwa Taj ɗin a tsakiyar goshinsa, kana ya daura hannunta tsakiyar kansa tare da cewa. “Marhababuka Yah Abana Barka da isowa lfy Allah ya Ubangijin yayi maka albarka”. Cikin tsananin jin daɗi ya ɗaura hannunsa bisa hannun mahaifin nasu tare da cewa. “Amin ya Allah. Yah Abana ya ƙafa?”. Ya ƙare maganar yana kallon Yah Abduraham dake ta murmushi, sai kuma ya maida kallonsa kan Yah Aryan dake yiwa mahaifin nasu masaj. Sai kuma ya juyo ya kalli Yah Aryan ɗin dake zaune gefe, yanayi mishi wani kallon dake cike da kishin irin tsananin son da mahaifinsu ke nunawa Taj ɗin. Sai kuma ya kalli Kabber wanda shine yaro na miji ƙarami a gidan nasu baki ɗaya. Shi kuwa Kabbir janye jikinsa ya ɗan tare da matsawa gefe. Da sauri Malam ya rike hannunsa tare da cewa. “A'a Kabir ina zaka je zauna nan kusa dani”. Ya ƙare maganar dayi musu murmushi dake nuna sonsu a ranshi dan baya ƙaunar su zargi cewa, yafi son wani a cikinsu. Hakan kuma yasa Kabir ɗin jin daɗi sai ya koma ya zauna a inda yake, shi kuwa Malam sai ya jawo hannun Taj ya ajiyeshi a gefen damansa. Maganar zuci Aryan ya fara yi. “Uhmmm ai dole dama shi Taj a gefen damanka zaka ajiyeshi, Kabir da shine ƙaramima kullum a gefen hagu kake ajiyeshi”. Yayi kalam cike da kishi. Shi kuwa Taj cike murmushi ya ɗago hannunsa tare da yafito yaran. Ɗuuu haka duk sukazo gabansu suka zauna. Mahira ɗiyar Yah Yusuf da kuma Iman ɗiyar Yah Hafiz ya ɗaura bisa cibiyoyinsa. Sai kuma ya jawo Islam ɗan yayarsa Maryam gabanshi. Yayinda saura kuma duk ya ajiyesu a ganshi. Dai-dai lokacin kuma Zakiya ta shigo da sallama Rashida da Maryam na biye da ita a baya. Rusunawa sukayi suka gaida mahaifin nasu da yayunsu. Kana Aryan da Kabeer suka gaida Rashida da Maryam dan sune manya a kansu. Gefenshi suka je suka zauna. Da sauri ya sa hannunsa ya amshi Trayn dake ɗauke da plates ɗin dake cike da fruit. Inabin ya fara sinka yana danƙawa yaran ɗaya bayan ɗaya, Tare da kallon Zakiya cikin sanyisa yace. Akwai jakar tsarabarsu, tana hannun Baba Abu Hashim, kije ki kwance kowa da sunansa a jikin nasa, ki basu, akwai kuma Chocolates insu, yana mota kije ki dauko duk ki basu”. To tace tare dasa hannun ta dauki Mahira da Iman. Haba su kuwa ƴan manyan jin haka keda wuya, duk sukayi ɗuuu suka bi bayan Zakiya suna faɗin. “Aunty Zakiya a fara ɗauko mama Chocolate ɗin”. Daga nan duk suka fice. Kusan duk Parlour da ido da murmushin suka rakasu. Shi kuwa Taj gyara zamansa yayi tare da kamo ƙafar Malam ɗin cikin sanyin sauti da halinsa yace. “Yah Aryan bari in karɓeka tausar nima in samu ladan”. Murmushi duk sukayi, shi kuwa Taj kafar mahaifin nasu ya daura bisa cinyarsa ya fara yi mushi tausa mai cike da iyawa a matsayinsa na likita. Sai kuma ya kalli Maryam dake cewa. “Ba abinda kacifa”. Sai kuma suka kalli Rashida da tayi saurin miƙewa tare da cewa. “Yauwa kin tuna min na, dama yau nace in sha Allah abincina Malam zai faraci”. Da sauri kuma suka kalli ƙofar shigowa jin muryar babbar yayarsu mai bin Yah Yusuf tana cewa. “Ai kuwa bamu yardaba”. Su dai sai murmushi suke haka ƴaƴan Malam matan da suke cikin Ƙasar Ethiopia a birnin Addis Ababa suka rinƙa shiga wanda yayanshi mata 13 ne cib maza kuma 7. Haka yasa yaranshi 20 ne cib. Sai kuma mata shi Huɗu, Hajia Halisa itace babba uwar Hafiz, sulaiman, Sai kuma Anty Khaulat sai autarta Hajara, sai kuma Hajia Sumayya itace mahaifiyar Yusuf da Aunty Ni'imatullah da da Aryan da Abdurahan. Sai kuma Hajia Muhibbat. Uwar Salma, Madina, Ruƙayya, sai Kabir, da , sai kuma Amal, Su ukun nada yaya 15 sai kuma Ummeey dake da biyar, Maryam, Rashida, Halima, Taj, Zakiya. Sune 20 cib. A irin ya wannan rana yakance da matansa, yau ranar ƴaranshi ne dan haka kada su matsa mishi. Dan duk ranar jumma'a ta ƙarshen wata duk ƴaƴanshi a tare suke wuni. Da sauri Rashida ta dauko womers ɗin ta da tazo dasu daga gidanta. Kana ta dawo gaban mahaifin nasu ta zauna tare da zuba mishi abinci. Halima da yanzu ta shigo hannun rike da womers ce tai ɗan murmushi tare da cewa. “Allah sarki gida daɗi, kunkam da kuke aure a garina kunji daɗi ai, irina dasu Aunty Ni'imatullah da Madina kam sai in munxo muke samun wannan ladan, dan haka tun da kan su tafi masallaci nayiwa Malam abinda zaici don nima in samu ladan. Yau dai kuyi haƙuri ku bari yaci nawa”. Murmushi mai cike da farin ciki malam keyi. Tare da kallon ahlin nashi, cikin fara'a Aunty Khaulat tace. “Gsky fa haka ne Halima to mun haƙura”. Da sauri Maryam tace. “Laah Aunty Khaulat ai wayo take mana, muda muke garin ai iya jumma'a jumma'a ne shima sai na ƙarshen wata kaɗai muke samu yaci girkinmu, sufa ƴan nesan nan in sunzo har su koma sukeyi masa girki. Irin Halima gata nan har shara side dinsa in dai tazo ita keyi mishi mu muna samun wannan damar ne”. Dariya sukayi duka sai kuma suka kalli Amal dake shiga tana cewa. “Kum tsaya mujadala gashi Aunty Rashida ta riga ta samu shi”. Ita kuwa Rashida murmushi tayi cikin jin daɗi kasancewar mace mai fara'a yasa Malam kan sake mata fuska sosai, cikin Murmushin ta mika mishi plate ɗin gashin da yaji Vegetables, da sauri Yah Yusuf ya amsa tare da ajiye mishi a gabanshi, Amal kuma Fruit ta ajiye. Mishi Aumty Khaulat kuwa sauran tarin womers ɗin dake kan Dinnin table nashi tasa su Halima da da Maryam suka jido da tarin plates and spoon's da fork. Nan duk ta zubawa, kowa. Hafiz ne ya kalli Taj dake tayiwa maifin nasu, tausa a ƙafarsa dake kusa dashi yana ɗan jan yatsun ƙafar, bisa dukkan alamu, yayi nisa a cikin tunani, domin ana ta mishi mgna yaci abincin Amman bai tan kana. Shi kuwa gaba ɗaya tunaninsa ya koma kan wancan al'amarin da ya faru tsakininsa da wacce tsohon nan ya buwaye su da kiran sunanta Adaya. Allah ya sani yana jin yunwa to Amman ina bazai iya cikin komai ba, domin cikinsa ya cika tib da ruɗani. “Afif me ke damunka”. Yah Yusuf ya tambaya cikin kulawa, eh dama Taj ba surutaccen bane kuma baisan kwaramniya Amman yanayinsa na yau ya nuna akwai wani abu tare dashi sai dai zurfin cikinsa ne bazai bari a gane damuwa bace. Cikin sauƙe nannauyan numfashi ya miƙe tare da cewa. “Bari inje inga Ummeey na”. Cikin kulawa Yah Hazif yace. “Ka zauba muci abinci tu...” Sai kuma yayi shiru ganin Mahaifinsu ya ɗaga mishi hannu alamun ya barshi, sai kuma yayi mishi nuni da hanya alamun yaje. Shi kuwa Taj ganin haka yasa ya fita, kai tsaye part ɗin Ummeynshi ya nufa. A Parlour kuwa cikin Rahama Amal tace. “Ke ma dai Aunty Maryam mutun da amaryarsa, kika san me ta shirya mishi, zaki wani da mashu da abinci kisa yaci ya koma ya kasa cin nata, kin kuma san Meymey da taɓara.” Kai Maryam ta jinjina ba tare da tace komai ba, sai mgnar zuci da tayi. “Uhmmmm Meymey ai ba irin wannan matar bane”. A can Parlour Ummeey kuwa zaune yake gabanta bisa kan Turkey carpet. Yayinda kanshi ke kife bisa guiwowinta, cikin kulawa da so tace. “Afif meke dumunka?”. Yah Salam wannan tambayar da sukeyi kishi tana kara ɗugunzuma nitsuwarsa, suna tuno mishi abinda ya faru. Ita kuwa Ummeeyshi ganin yadda jikinshi yake a mace ga idanunsa da su ɗanyi ja ga alamun rashin nitsuwa, sai tayi tunanin ko begen matarsane, haka yasa cikin kulawa tace. “Toh yanzu dai tashi ka tafi gidanka. Ka dawo gobe muyi hira”. Yes Allah ya sani so yake ya kaɗaice, ko zai samu damar da zai yi nazari. Hakan ne yasashi ɗago kanshi a hankali. Ido Ummeynshi ta zuba mishi tana nazartar yanayin tashin hankali da ɗimuwar dake cikin eyes ɗinshi. Ta sani bazai faɗa komai ba saboda tafi kowa sanin tsananin zurfin cikin ɗan nata. “Babana meke faruwa ne ka gaya min mana”… Cike da juriya ya ƙaƙalo murmushi dole wai dan ya kwantar mata da hankali cikin sanyi yace. “Ummey na ba komai fa kwai gajiyace”. Kai ta jinjina tare da ɗago hannunsa kana tace. “Toh muje ka gaisa dasu Hajia Babba sai ka wuce gidanka ka samu ka huta”. Ba musu ya bita a baya suka shiga sashin matan baban nashi sai dai basa ciki alamun sun tafi wurin Malam haka yasa suka wuce can. Bayan ya gaida su ne yayi musu sallama. Kana Ummeey da da yayunshi Rashida da Maryam da Aumty Khaulat suka rakashi. A bakin motar suka tsaya suna ɗan hira saboda, hango Abu Hashim dasu Baba Idi suna cin abinci. Shi yasa suka ɗan zauna suka jirasu. Suna gamawa Abu Hashim yazo. Kana su Ummeey suka koma ciki. Motarsu na gab da fita motar Uncle Jibirin na shigowa. Haka yasa Taj cewa. “Abu Hashim tsaya”. To yace kana ya tsaya shi kuwa da sauri ya fito tare da nufar motar Uncle Jibirin da tuni sunyi parking har driver'nsa ya buɗe masa ƙofa ya fito, Dottijon ne da bazai gaza Malam ba. Cikin tsananin sakin fuska ya nufi Taj yayinda shima Taj shi ya nufa. Rusunawa yayi ya gaidashi. Ya amsa a mutumce kana ya ɗaura da cewa. “Amman Mamana bata san ka dawo bako Taj, dan yanzu haka can gidan naka na fito bata gaya min cewa ka dawoba”. Kai ya ɗan rusunar tare da cewa. “Ai isowata kenan. Ko Malam bai san zan dawoba ganina kwai sukayi, yanzu zan wuce gidan”. Motsawa Uncle Jibirin ɗin yayi tare da ɗan bubbuga kafaɗarsa kaɗan kana yace. “Toh aje a huta”. Daga nan shi yayi cikin gida, shi kuwa Taj ya koma cikin mota suka nufi gidansa da ba wani nisa sosai dan kusan sashin layin wurin duk su ya sune, gidan babansu suka sa a tsakiya duk su mazan gidajensu na zagaye da na babanne”. Uncle Jibirin, aminine ga Malam wanda duk wanda yasan Malam a Ethiopia ya sanshi ne da Jibirin, bashi da kowa a duniya da ya aminta dashi sama da Jibirin bashi da abokin shawara a duniya sama da Jibirin. Shine iya kar wanda Ƴayansa kab suka sani wai wani na jikin mahaifin nasu, basu san kowa nashi a duniya ba. Sai Uncle Jibirin, shine madadin Babpansu kakansu kakarsu. Wanda sunayensu kadai suka sani, wanda Taj yaci sunan kakansu na mijin. Halima kuma taci sunan kakarsu macen. Wannan yasa komai na abinda ya shafi aure Uncle Jibirin keyi musu da kuma Sheykh Adam wanda shine kuma amini na biyu a wurin Malam kuma shi ke ja mishi baƙi. Wata Shida Baya Malam da Uncle Jibirin suka haɗa auren Taj da Meymey ɗiyar Uncle Jibirin ɗin wacce taci sunan kakanta, wanda bisa dole suka datse soyayyar da Meymey keyi da wani Dr da suka shafe cekara biyu suna soyayya. Taj kuma baima saniba kawai dawowa yayi ya samu Meymey, wai ai an aura mishi ita, wannan al'amari yayi misifar hautsuna mishi lissafi ya watsa mishi dukkan wani ƙudirinsa. Toh Amman su kansu dan sanin biyayyarsa da haƙurinsa ne, yasa sukayi mishi haka, koda ya dawo kuma Malam da kanshi ya kaishi gidan da aka shirya mishi matarshi kuma take can. Ita ko Meymey ta lashi tokobin sai ta kashe auren ko ta wacce hanya. Tayiwa kanta alkawarin babu abinda zai rabata da Dr Zakariyya, domin shi takeso, ta shirya ko ta wacce sigar sai ta rabu da Taj. Wanda shi baima san tanayi ba domin ya lura Meymey makirace, bata saniba shima bawai sonta yakeba, Amman kuma bazai tozartata ba. A hankali ya tura ƙofar falonta, Tare da kutsa kanshi cikin Parlour. Sassayan numfashi ya fesar ganin yadda Parlour ke hargitse bisa dukkan alamu ba ita da Laylah kaɗai bane a cikin gidan. Cikin ɗan ɗaga sautin murya kaɗan ya fara kiran Laylah ƙawar Amininshi Irfan Imran dan Palastine ɗinnan. Wace take cike da marci gaba da baya. “Laylah Laylah Laylah!!!”. Ya ƙare kiran sunan nata da ɗan ƙarfi. Wanda hakan yasata fitowa daga kitchen a guje ta nufoshi. Sai kuma ta tsaya turus a gabanshi. Tuni idanunta na tsatstsapo da hawaye, tuno yadda Irfan keyi matansa yasashi buɗa mata hannayensa. Da gudu ta ruggume ƙafafunsa. Cikin kula da jinta cikin tsatson jinkinsa tamkar yar da aka haifesu ciki ɗaya a tausashe yace. “Me kikeyi a kitchen?”. Ya ƙare maganar yana Binta da ido ganin yadda ta rame har ta ƙanƙance. Cikin murmushi tace. “Indomei zan dafa inci yunwa nakeji”. Kanshi ya ɗan jujjuya tare da kallon tsakiyan Parlour. “Ina Antynki?”. Da yatsa ta nuna mishi bedroom ɗin Meymey. Kafaɗunta ya ɗan riƙe tare da ɗan matsar da ita gefe, kana ya nufi inda ta nuna mishin. Tura ƙofar yayi a hankali tare da shiga da sallama a bakinsa. “Assalamu alaiku....”. Sai kuma rogowar sallamar ta maƙale a tsakiyar maƙoshinsa bata koma cikiba kana bata fito wajeba. Sai kuma ya tsaya tamkar an dashi idanun sa kuwa sai neman rufewa sukeyi da kansu, saboda sai ƙanƙamcewa sukayi, ya kuma hanasu rufuwan ya saitasu, kan Meymry dake ruggume da Dr Zakariyya! Wani irin tsuma da tashi yaji tsikar jikinsa nayi. Wanda yake da yaƙinin bakwai na kishi bane, sai na tsananin mamaki da jin tsoron lalacewar Meymey, eh ya sani makirace, Amman bai taɓayin zato ko tsammanin cewa lalacewarta har ta kai matsayin tayi wannan muguwar ɗabi'a da kuma igiyoyin aurensa a tsakiyar kantaba baisan cewa rashin tsoron Allah ta ya kai wannan mata kinba ta shigo mushi da gardi fasiƙi mazinaci har cikin gidansa,. Dr Zakariyya kuwa, wani irin fitinenne fitsari tsorone ya tsinkomishi. Saboda kwarjini da haibar Taj ya tsinka mishin hanjin ciki da zuciya. Wannan yasa tuni fitsarin ya fara ɗiso mishi cikin sauri yayi ƙasa da kanshi domin bazai iya kallon tsarkakkun idanun Taj da nashi ƙazanrattun idanunba. Ita kuwa Meymey cikin wani irin tsaurin ido da tson ɓoye ainihin firgita da gigitar da tsoron idanun Taj daya sakar Mata, tasa hannunta da sauri da nufin kamo hannun Dr Zakariyya daya janye jikinsa da nata, yayinda gaba ɗaya jikinsa yake ta rawa tamkar mazari. Sai kuma ya nufo hanyar fita yana wani irin yin fiki-fiki da munafukan idanunsa. Shi kuwa Taj a hankali ya ɗan jungina da gefen ƙofar tare da harɗe hannunsa a ƙirji kana ya ɗan ɗaura ƙafarsa ɗaya bisa ɗaya. Kululu'ulllllllluuu. Cikin Dr Zakariyya da Meymey suka bada sautin a tare. Shi kuwa ido ya kafe Meymry dashi ba ko kebta wannan ne kuma ya sakar mata da rawan jiki. Shi kuwa Dr Zakariyya cikin fellewa a guje ya raɓa gefen Taj ɗin ya wuce. Yana matse da hantsar wonɗonsa da tuni ya jiƙe da fitsari. Da wani irin kallon da yasa hantar cikin Meymry kaɗawa ya raka Dr Zakariyya dashi. Sai kuma ya dawo da lannsa kanta, ko ƙala bai ce mata, sai irin kallon nan. “Ke najasace, kuma ke baki da amincin da zuciyata zata aminta dake bare inji kishinki, sai dai inji kishin saɓawa Allah da kikayi a cikin gidana”. Duk da ba mgna yayi da bakiba Amman idanunsa sun nuna mata kallon ƙazantacciya kuma ƙasƙantacciya yakeyi mata. Wani irin rumtse idanunta tayi da ƙarfi lokacin da taga ya juya ya fita. A Parlour ya samu Laylah riƙe da plate ɗin indomei. Hannunta ya kamo kana ya juya suka fito. Ganin ya shiga Motane yasa Abu Hashim shigowa ya ja motan tare da cewa. “Ina zamuje?”. A taƙaice yace. “Gida”. Koda suka isa cikin gidan, kai tsaye part ɗin Malam Laylah ta nufa, shi kuwa part ɗin Ummeynshi ya shige. Laylah na shiga Halima ta buɗe mata hannun da gudu tazo ta, ruggume sai kuma tayi saurin sake Halima ta ruggume Ummeey tare da cewa. “Ummeey yunwa nakeji”. Cike da tausayin tarin maraicin dake dabai-baye da rayuwar yarinyar Rashida tayi sauri sa mata abinci. Maryam kuma kama hannunta tayi ta zaunar da ita. Nan take ta faraci, hannu baka hannu ƙwarya, fes ta cinye ganin haka Rashida ta ƙara mata. Shima tas ta cinye, za'a ƙara mata ne, tace a'a ya ishe ta. Cikin kulawa Halima dace. “Laylay kin rame kinyi doshe da yawa”. Kai kawai ta jinjina tare da ɗaukar Iman suka fita, ta nufi gardin ɗin gidan. Ganin lokacin sallan la'asar ya ƙaratone yasa. Malam da Uncle Jibirin da suke ɗaya Parlour suka fita suka tafi masallaci kamsussalat dake cikin gidan. Haka yasa suma duk mazan suka fita. Su kuwa mata hira suka ɗan ci gaba dayi saboda da ɗan sauran lokacin. Sai da suka ji an kira sallane, kana duk suka miƙe suka yi sallan la'asar ɗin a nan Parlour Malam, bayan sun idar ne kuma duk suka miƙe suka nufi sashinsu. Maryam da Halima ɗakin da Haliman ta sauka suka nufa, Rashida kuma bayan Ummey tabi, dan zata kimtsa mata durowarta. Cikin wani irin yanayi mai wuyar fahimta Ummey ta ke kallon Taj dake zaune bisa alamu yanzu ya dawo daga masallacin. Zaune yake a ƙasa yayinda ya kife kansa bisa gadon, tare dasa hannunshi duka biyu ya rumtse kanshi dake mishi wani irin fitinenne sarawa, sam shi lamarin Meymey baya cikin kansa, sai wannan gangancin da yafi kama da wasan kwaikwayon da ya aikata ne, ke gab da fasa minshi kai, a hankali ya ɗan murza kanshi kaɗan ya gyara wayar dake manne da kunnenshi. “Uhmmmmm”. Ya fidda wani sauti mai kurman baƙi. Aysha kuwa gyara zamanta tayi, tare da gyara wuyan ɗan ƙaramin baby hijjab da su Doctors suke yawan ta'ammali dashi. Sai kuma ta lunshe idanunta tare da gyara riƙon wayar d takeyi da Taj ɗin, cikin sassayan murya tace. “Please ka daina wannan damuwar, in sha Allah ba wata matsala da zata faruwa, yadda ka tsaida hawayen dottijon nan, Allah zai cika maka rayuwarka da farin ciki ya tsaida ma hawayenka, na sani yanzu ko abinci baka ciba”. Sai kuma ta buɗe idanunta jin muryar Dr Nafi'u Kabir Katsina ya turo ƙofar Office ɗinta tare da cewa. “Hi Sweetheart me kikeyi ne, har yanzu baki tafi gidaba?”. Wani ɗan gajeren tsaki Taj yaja saboda jin Muryar Dr Nafi'u Kabir Katsina. Sai kuma yayi saurin sakin sassayan numfashi tare da mgnar zuci. “Wai kai Taj meyasa kake tsanan kusancin Dr Nafi'u ne, da Ishmah duk da kasan cewa ta tsaidashi a matsayin mijin aurenta, wanda yau saura wata ɗaya ne rak aure nasu”. Sai kuma yayi saurin buɗe idan shi jin Muryar Ummeynshi. Zama tayi gefenshi kanshi ta ɗan ɗago tare da ɗaurawa bisa cinyarsa, cike da kulawa tace bani wayar. Ba musu ya miƙa mata Katse kiran tayi domin bata san da waye yake mgna ba, sai kuma ta kalli Rashida data zuba musu ido. “Jeki duba a fridge din Dinnin area akwai fruits salat da na haɗa, ɗazu ki kawo min”. To tace tare da juyawa ta fita. Jim kaɗan da fitanta ta dawo hannunta riƙe da wani bowl mai ɗan kare kyau, da spoon a ciki, amsa Ummeynshi tayi tare da ɗan janye guiwowinta, kana ta fuskanceshi da kyau, ɗiba tayi tare da kai mishi baki. Kai ya ɗan jujjuya sai kuma ya miƙa mata hannun alamu ta bashi, zaisha da kanshi. “Ka tabbatar?”. Ta tambaya cike da so ƙauna kulawa irin na uwar, uwarma da shi kaɗaine ɗanta na miji. Ganin ya gyaɗa mata kaine yasa ta miƙa mishi. A hankali ya kai spoon ɗin bakinsa. Spoon biyu yayi sai kuma ya ajiye, ganin haka ne yasa Ummeynshi amsa ta fara bashi, dole ya fara amsa saboda ganin alamun rashin cin abincin nashi na damunta. Saida ta bashi kab kana tace. “Zuwa yanzu zurfin cikinka, ba damuna yakeyi ba, cutar dani yakeyi, Afif ina cutuwa da zurfin cikinka da haƙurinka. Zuciyata na ƙuntata a duk sanda naga tarin damuwa tare da kai, Amman sai kaƙi faɗa. Har kwanan gobe nasan cewa ba son Meymey kakeyi ba, Amman tsananin haƙurinka da zurfin cikinka yasa mahaifinku gaza gane abinda kakeso da wanda baka so, har ya aura maka matar da ranka bayi so. Still yanzu kuma naga tsananin tashin hankali a cikin ƙwayar idanunka da ɗimuwa, Amman kayi shiru ka binneshi a ranka ya kakeso inyi ne Afif?”. Wani makararren murmushi ya ƙaƙalo ya ɗaura bisa fuskar da bata taɓa riskar irin yanayin damuwa da yake cikiba sai lokacin da aka aura masa Meymry da kuma yau. Cikin son kwantar mata da hankali da gudun ɓacin ranta yace. “Ummey na ba abinda ke damuna fa, kwai gajiya ce, so nake nayi bacci”. Da sauri tace. “Toh me ya dawo da kai bayan ka tafi gidanka”. Cikin sanyi yace. “Laylah ce na samu, bata ci abinciba Ummey shiyasa na taho da ita taci abinci in kuma yi sallan la'asar da Yah Abana”. Ido kawai ta tsura mishi tana son nazartarsa, Amman ina shi har idanunsa kan iya ɓoye ainin matsalarsa duk duniya ita ɗince ma kaɗai kan iya fahimtar yana cikin wani yanayi ma, sai kuma Ishmah da ita ko muryarshi taji tana iya gane komai tare dashi. Ajiyan zuciya mai tafe da raunataccen numfashi ta fesar tare da fara mishi addu'a. “Yah Allah ka shiga lamarin wannan ɗan nawa Tajuddeen, ya Allah kaine ka halicce shi da zurfin ciki, da haƙuri da jurayar da tasa baya iya fuskantar kowa na duniya ya faɗa masa matsalarsa sai kai, mahaliccin mu, Yah Allah ka shiga lamurran sa ka yaye mishi damursa ka bashi sa'a da nasara akan duk wani ƙalubalen rayuwa, yah Allah ka hana hawayensa zuba a inda bashi da mai sharce mishi su”. Murmushi nan dai na ƙarfin halin yakeyi yana mai amsa addu'o'in da take jere mishi, hakama Rashida da Maryam da yanzu ta shigo. Hannunshi ya miƙa Ummeeyshi tare da yin musabaha kana ya miƙe tsaye. “Bari in tafi”. Tana miƙewa itama tace. “Toh Laylah fa?”. Yana mai ɗan taune gefen lip inshi na ƙasa yace. “Zamu tafi tare?”. Ya ida mgnar suna fitowa Parlour, dai-dai lokacin kuma Zakiya da Laylah suka shigo, haka yasa suka fita tare. Suna isa gidan. Ya wuce side ɗinsa. Laylah kuwa cikin sanyi ta nufi bedroom ɗin Meymey dan zata isar da saƙon Halima. Daga bakin ƙofar ta fara jiyo Muryar. Amal ƙanwar Taj ƴar Hajia Muhibbat, uwar Kabir kenan wanda itama ƴaƴanta duk matansae sai Kabir kaɗai Cikin neman mafita da kuma saka gadar zaren da suke shiryawa Taj Meymey tace. “Ai wallahi ko yaƙi Allah sai ya sakeni, ko shine ƙwai sai na sashi ya magantu, kuma zanyi amfani da zurfin cikin nasa, da ya hanasa fitowa ya butulcewa iyayensa lokacin auren harfa wani cemin yayi nimafa ba sonki nakeba. Kawai kije ke ki butulcewa naki mahaifin nasan in kikace bakya so Malam zai janye”. Ƙwaffa Amal tayi tare da cewa. “Bana gaya miki tun lokacin ba, inda Yah Afif ne, wlh bazai taɓa yiwa Malam musuba, ko ya fito da damuwarsa, haka Allah yayisa. Shi yasa da wannan halin yasa Malam yakeyi mishi wani irin bayyannen son da bai san cewa fuskarsa bata iya ɓoyewa ba, ke Yah Afif duk nacinka da jarabaar neman mgnarka bazaiyi ma kamar yasan kanayi bare ya kulaka, domin da yana kula mutum da tuni shi da Yah Aryan ko mgna bazasuyi ba, domin a fili yah Aryan yake nuna tsananin tsanar da yake yi masa. Kuma abin mamaki yanzu haka shi ya ɗauki nauyin karatun Arfa, ɗan Yah Aryan wanda pilot yake karanta in kinji milliyoyin da yake kashewa sai ki riƙe baki. Ya haɗa da Imran ɗan Yah Hafiz, duk shi yake musu komai suna karatu a Mexico”. Sai kuma ta zuwa Meymey ido jin tana cewa. “Uhmmm ai bai haɗu da kaidin macce bane, su mazane shi yasa”. Da sauri Amal tace. “Kaidin macce kuma ai in kinsan abinda Mom ke shiryawa a kansa tsawon shekaru yana tsallake wa sai kinyi mamaki. Kawai dai yanzu zamu haɗa ƙarfi da ƙarfe ne. Zan gayyato Yah Aryan da Mom a cikin tafiyar. In sha Allah sai mun tozartashi tozarci mafi muni, sai mun Ƙyamatar dashi a zuciyar Malam sai mun rabashi da wannan soyayyar ta juye ta zama ƙiyeyya, uwarsa kanta da take jin daɗin ɗanta mahaddacine sai ta fara kunyar amsa sunan uwarsa sai tayi nadamar haifarsa”. Wani makirin murmushin Meymey tayi tare da gyara zamanta suna masu ci gaba saƙa gadar zare. Laylah da tazo da niyar, isar da sakon Halima na ta cewa Meymey gobe zatazo ta wunin musu. Jin kalaman da sukeyi ne, yasata tsayawa a bakin ƙofar tamkar an dasata. Duk da ƙaramcin shekarunta. Abun ya bugeta, haka nan tsoron Meymey ya ƙara rufeta. Jin motsinsu alamun zasu fitone yasa tayi saurin fara yin Knocking. Dai-dai lokacin kuma suka iso bakin ƙofar Amal ce a gaba, ganin Laylah ne yasata ɗan suƙe fuska tare da cewa. “Lafiya”. Cikin yin ƙasa da kai ta isar da saƙon Halima, da sauri ta juya da baya saboda tsawar da Meymey ta watsa mata. “Ke matsa daga nan shegiya ƴar ta'adda ɓacemin daga nan”. Da sassarfa ta wuce ɗakinta. Shi kuwa Taj yana shiga al'wala yayi tare zama bisa sallaya, idanunsa ya lumshe tare da fara karanta suratul Khaff. Sai da ya dire ayar ƙarshe sai kuma, ya saita Camera wayarshi. Ya karanta aya ta 67-70, ya tura a shafinsa na TikTok Tare da ɗanyin ɗan guntun rubutu a saman video. Don't forget to read, suratul Khaff on Friday, Jumma'at Mabrooq to all Muslims Ummah. A ƙalla yayi kusan stsawon shekara ɗaya da fara hakan, domin tunasar da al'ummar musulmi. Yanayin Update ɗin video in 5 minutes a ƙalla mutum sama da 1,700 sukayi mishi like, a comment kuma sama da mutum 1000 ne sukeyi, mafi akasari su addu'o'i garesa da jinjina baiwar zazzaƙar muryar da Allah ya bashi. Follower's kuwa duk ta inda al'ummar musulmi suke a duniya waɗanda ke TikTok ɗin suna biye dashi. Misalin ƙarfe sha biyu na dare. Ishmah ce ke kwance bisa gadon ta, tayi da take riƙe da wayarta tana bibiyar comments ɗin da ake yiwa Taj, wanda dama ita ke bibiyar masa comments inshi, duk abinda ta gani na tambaya ko yabawa ko neman haske, takanyi screenshot sai ta tura mishi ta Whatsapp. Washe gari ranar asabar. Cikin Ethiopia, gidansu Adaya. Daga bakin ƙofar Parlour wani, irin kiɗinema mai cike da salon kiɗin su na Ethiopia na Damm ke tashi. Zirya takeyi a tsakiyar Parlour tare da rawa da juyi tamkar mazari, irin rawarsu nan dai na wuya da kafaɗu. Cikin burgewa da so, ganin sabanin kwarewar ta a rawar, ƙawarta Asina da abokinsu Izzin, suke kallonta, dayi mata video tare da liƙi, jujjuya kanta takeyi, tana tsawo dashi, kamar barewa, sai kuma tayi guntu dashi kamar, kwaɗo tana jujjuyashi kamar maciji, sai kuma fara karkaɗa kafaɗarta na hannun hagu, kai kace jikinta ba ƙashi bane, robace, pantsama-pantsaman nononta kuwa sai rangaji sukeyi cikin yar rigar data matsesu, tamkar zasu bulluƙo waje dan girma da cika, sunyi tumsu tumsu. Izzine, ya kalleta cike da sha'awa domin yana masifar gigita da yadda take kaɗa rusa-rusa nonon. Sai kuma ya haɗiyi yawun , saboda ganin yau ɗin tana cikin tsananin fushi da hatsala tana rawan ne domin shine kaɗai ke sama mata nitsuwa, cikin haki ra Fuskan cesu, cike da yanayin ƙunci mai gwauraye da tsiwa da gausin baki dake bayyana shagalarta da duniya, ta dawo ta zauna gaban Step Mom ɗinta. Tare da rumtse idanutan da kukan data kwanayi yayi sanadin kumburarsu cikin yaƙini da ƙarfin aniya cikin harshen Yaren Omoro tace. “Wallahi tallahi auren nan bai ɗaur.... Wasan da yanzu aka soma, toma me akayi ki biya ki karanta cikin salama. By *GARKUWAR MARUBUTA* [1/7, 12:14 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 5* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin INDA RAI na kiɗine wannan free pages ne, muna gama free page kuma ko kin ganshi a wani wurin to na satane, ki biya ki karanta cikin aminci da salama 1k ne kacal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. Mutanen kasar Niger kuma 1000fc ne kacal zaku biya jaka ɗaya kenan +22790899076 ga number mommy ta wurinta zaku biya* Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Kayana sun iso lfy. Aikin su ya kankama, komai ya zama Available. Duk abinda kake so a cikin wanda zan sako a nan akwaisu Available, kayane masu zafi da tururi kayane da ban taɓa jibgo kamar su da irinsu ba. Ku matso iyayen amare, da amaren da yayun amare da ƙannen amare da ƙawayen amare, Uwar gidaye gareku, tsakar gidaye kuma ban barku a baya ba, mai jego sabon haihuwa ko tsohon jego wato barden goyo, amarya Budurwa ko Bazawarara duk ku taho kowa da zazzafan haɗinsa, ina araha kam duk ɗan karen tsadan da kayan suka ƙara Amman fa ina hana bashi ga number da zakiyi min mgna 08069423567. kaya ne mata mai tsuma jiki da ratsa jiki. Kayana set ne hawa hawane, akwai manyan set akwai ƙananan set ƙanan daga 40k 35k 30k 25k 20k 15k 12k ƙaramin ƙarshen 5k sai kuma manyan set ɗin daga 50k ne zuwa sama 60k 70k 80k 90k sai sha kunɗum ɗin 100k. Kana akwai kayan ƙamshi ma suma haka ne farashin su. “Ɗauru a kaina ba, na gaya muku, babu aure a jadawalin rayuwata a yanzu, inada burin zama shaharerriyar ƴar rawa a rayuwata, aure zai hanani cika burina, shiyasa duk auren da Abpu ya shirya yi min, nida kaina nake watsashi. Sannan yau rana tsaka in gama shirya yadda auren zai watse, na kuma yi nasara ya watse, sannan a samu wani jarabbeben mutum ya faɗo sama ta ka, a rana tsaka yace, wai ya aurawa ɗanshi ni, toh wlh tallahi sai yayi nadaman aurawa ɗanshi ni. Domin asarar kuɗin sadakinsu da goronsu kawai sukayi, ni dai Adaya ba aure a tsarina a yanzu.” ta ƙarashe mgnar tare da miƙewa tsaye taci gaba da wani irin rawa da karya ƙugu tamkar mazari. Ita kuwa Ummi wacce ƙanwace ga mahaifiyarta, bayan rasuwar mahafiyar Adayan ne aka aura wa babanta ƙanwar mahafiyar tata, domin tazo ta riƙe ƴaƴan ƴar uwarta, Adaya Aminullah, saboda an san abokiyar zamanta mahaifiyarsu Ma'aruf bazata riƙesu ba, saboda tsananin kishi. Cikin zubda hawayen da suka cika kwarmin idanunta ta riƙo hannun Adaya tare da cewa. “Adaya ki zauna, ki saurareni, da kunnen basira zaki gane cewa, mahaifinku gata yayi Miki, duk ranar da baya raye, zakiyi kukan da babu mai share Miki hawayenki, wannan rayuwa da kikeson sa kanki bafa rayuwace ta Musulmin ƙwaraiba, na roƙeki da Allah Adaya ki duba makwancin ƴar uwata mahaifiyarku, ki zame mata al'waladussaliha kamar yadda Aminullah ya zame mata”. Sai kuma ta rumtse idanunta saboda jin Adaya ta janye hannunta tare da cewa. “Ummi ba aure a tsarina, kuma ko zanyi aurema ai sai a bari sai lokacin da nayi ra'ayi na kuma fidda wanda nakeso, bawai haka nan auren haɗiba, kijifa Izzin yana ce min, roƙo da magiya da kuka Abpu ya rinƙayi a cikin Masallaci sai kace irin na zame mishi masifa da bala'i a gidansa Allah Allah yake ya rabu dani”. Sai kuma taje gaban kayan kiɗin nasu tare da ƙure sautin. Ita kuwa Ummi juyowa tayi ta kalli Izzin cike da tsanar abotarsa da Adayan, domin shine yake ƙara ingiza ta, gashi Adaya da ɗan karen taurin kai da kafiya, duk zafin mahaifinsu da tsananinsa akan yara ta buwaye sa, ya gagara tan kwarawa, zuwa yanzu gani yake aurene kaɗai matakin ƙarshe da ya rage na samun damar tankwaratan. Sai kuma Asina da ita kanta Ummi bata gane alƙibilar Asina. Cikin tsuke fuska tace. “Izzin an kira sallan azahar ya kamata ka tafi masallaci”. Ta ƙare maganar fuska a haɗe, hakanne yasa Izzin kallon Adaya tare da ɗanyi mata signal kana ya ɗan kai hannunsa bisa kunnensa alamun sai sunyi waya. Ita kuwa Asina jan hannun Adaya tayi suka nufi bedroom ɗinta. Ita ma Ummi nata Bedroom ɗin ta nufa. Suna shiga Anisa ta kalli Adaya, tare da yin murmushin tace. “Mrs Tajuddeen, ko ya yake Tajuddeen ɗin naki, mai ajine ko garma-garma ne, wayeyyene ko kifeffe ne, to wai ma Adaya kin shiryawa zama da namiji a yanzu ne”. Ciki da takaici da ƙara hatsala tace, koma shi wanne irine zai zo ai ya sameni, daram duk yanayin da naga yake dashi, ai dashi zan yaƙeshi in sashi ya sakeni. In shi ustas ne, in nuna mishi ni karuwace, zuwan farko in nuna mishi ni mayatacciyar na mijine, in shi mugune in nuna mishi na fishi mugunta, in shi na kirkine in nuna mishi ni ta banzace, Kinga ba ɓata lokacin zai sakeni, kin san gasan rawar da za'ayi a India ina cikin team ɗin ethiopia.“ Cikin jinjina kai Asina tace. “Nasan kuwa muddin kina cikin team ɗin mune zamuyi nasarar lashe gasarar rawa na duniya baki ɗaya a shekarar nan, domin ke ta musamman ce”. Daga nan dai sukaci gaba da hirar rawarsun. A cikin sharara gudu ishmah key tuƙin, ta fito daga Jada ne zata dawo cikin Jimeta, Gudun takeyi cike da ƙwarewa da iyawa, yayinda waya ke maƙale a kunnenta. Sai gefen mai zaman banza kuma da Aunty Hauwa ke gefentan ƙanwar Dadeey mai binta. Dai-dai lokacin kuma Taj ne da Laylah ke zaune a Parlour Addawa, gefen Taj ɗin ta zauna tare da jawo Laylah jinkinta, cikin tausayawa tace. “Kin ƙoshi ko?”. Kai ta jinjina mata, tare da cewa. “Amman Uncle Taj bai ciba Addawa”. Kai jinjina mata tare da cewa. “Ai indai yana waya da Ishmah baya jin yunwa, sai ya gama zan ɗan gasa mishi nama yaci”. Murmushin tayi tare da cewa. “Addawa Aunty Ishmah nada kirki, tana sona, tafi Aunty Meymey sona”. Murmushi Addawa tayi tare da zuwa Taj idanu tana sauraron hirarsa da Ishmah. Cikin Lumshe idanunsa tare da tausasa muryasa a hankali yace. “Wai ina kika jene baki gaya minba Ishmah”. Cikin sauƙe numfashi tace. “Afwan Taj jikin Dadeey ne ya tashi jiya kwana mukayi bamuyi bacciba, sai ƙarfe huɗu asuba jikin ya lafa, so naje Jada ne amso mata magani”. Ta ƙare maganar cike da rauni da alamun damuwa. Sassayan numfashi ya fesar cike da tausayawa da son Dadeey cikin ransa, cike da kulawa yace. “Ayyah Dadeey Allah ya bata lfy yasa ciwon nan ya zame mata zakkan jiki, kuma kaffara Allah ya yaye mata. Cikin sanyi tace. “Amin ya Allah”. Tayi mgnar tana gyaɗawa Aunty Hauwa kai saboda jin tana cewa. “Taj ko?”. Ganin ta gyaɗa mata kai alamar eh shine, yasata yin murmushi. Gyara zamansa ya ɗanyi saboda jin sosai yau ɗin take da sanyi, ya fahimci sosoi jikin Dadeey ke damunta. “Kina jina”. A hankali tace. “Eh Taj”. Ɗan Murmushin yayi domin ya gama sanin tana masifar son sunnshi tunda har alƙawari tayi mishi in tayi aure ta haihu zatayi mishi takwara. “Ko zamu fita India da Dadeey ne?”. Cikin sanyi tace. “Hmmm Taj ka mance ne, jinin da yawu da komai na gwajin cuta na Dadeey an ɗiba an kawoma Ethiopia ka gama bincike a kai, ka turashi India aka gama bincike akai, ba'aga me yake damumtaba duk gwajin da akayi result ɗaya yake badawa, bata da matsalar komai”. Sai kuma ta fesar da zazzafan numfashi tare daci gaba da cewa. “Kaida kanka da Dr Khumar Kapoor kuka tabbatar min cewa, jinyanta bana asibiti bane”. Cike da damuwa yake jinjina kai domin ta tuna mishi irin yadda suka binciki kamai na Dadeey Allah baisa sun gano matsalarta ba, kuma sosai ciwon yafi kama da matsalar iska. Domin yanzu jikin zai riƙece, ko zama bazata iyaba saboda jiri anjima kaɗan ka sameta garau, ga masifar ciwon baya, tafiyarta duk ta sauya saboda ciwon da yake riƙe jijiyoyin ta, hatta hannunta basa iya taɓa ko bayanta duk suna son ƙandarewa. Cikin sanyi yace. “Amman kunayi na Islamic ko?”. Da sauri tace. “Eh shine”. Dai-dai lokacin kuma ta iso ngurore zongon baƙi, cike da nitsuwa ta karya kwana tare da ɗaukar hanyar da zai sadata da cikin jimetan. “Yauwa my Ishmah a kiyaye irin wurin da za'aje neman maganin, domin shi cuta jarrabawa ne, in kayi halattacen jinya baka faɗa wurin bokaye da ƴan bori da masubbataba, to shine sai ya zamewa majinyaci kaffara, kuma kuma ku samu ladan jinya, domin da Dadeey da Abba dake dasu Yah Abubakar da Hamisu dasu Adam duk Allah ya jarabceku da cutar Dadeey ne to kuyi ƙoƙarin cinye Jarrabawar, ta hanya mai kyau in sha Allah watarana zai wuce”. Sharce hawayenta da ya gangaro mata tayi tare da cewa. “In sha Allah kuwa Taj, ngd”. A hankali ya lumshe idanunsu saboda jin muryarta na rawa alamun zatayi kuka, fahimtar hakanne yasa cikin sauri yace. “Ga Laylah”. Jin haka kuwa yasa Laylah amsar wayar tare da cewa. “Assalamu alaikum Aunty Ishmah nayi missing naki, tunda Uncle Taj ya tafi bamuyi wayaba”. Cikin sauƙe numfashi ta ɗan saki guntun murmushi tare da cewa. “Miss You to my Laylah Uncle Taj ne ya hanani number Meymey da zanyi ta kiranki ta nan muna gaisawa”. Cikin jin daɗi tace. “Toh zan baki number Ummeey mu rinƙa gaisawa da wayarta”. Cikin sanyi tace. “To ba matsala”. Ita kuwa Laylah cekin sonta tace. “Aunty Ishmah yasu Khalid da Minat”. Cikin jin daɗi tace. “Suna lfy yauma zasuzo gida Kinga yau weekends ne”. “Ayyah Aunty Ishmah in kin koma ki haɗam..” Bata kare mgnar ba ta miƙa mishi wayar ganin yana miƙo mata hannunsa. “Uhmmmm komai iri ɗaya ko?”. Ɗan murmushi tayi tare da cewa. “Toh me kuma yayi iri ɗaya?”. A hankali yayi mgnar murya can ƙasa yadda Addawa ma bazata jiba yace. “Zuwa yanzu na yarda komai namu ɗaya ne Ishmah, kinga nima banyi bacciba kema bakiyi ba”. Tana mai ɗan rage gudunta sabida cunkoson ababen hawa tace. “Uhmmm haka fa, to ni dai fatana abin farin ciki ne nakeso ya rinƙa zuwa mana a tare ba akasin hakaba, kagafa komai sai ka raɓa min”. Murmushi gefen baki yayi sai kuma ya buɗe manyan idanunsa dake lumshe jin tana cewa. “Fatana dai ka raɓa min aure, nima in samu aurena da Dr Nafi'u ya tabbata kada ya watse kamar saura”. Fuska ya tsuke tare da cewa. “Hghhmmmm”. Sai kuma ya kauda zancen da cewa. “Jiya ba'ayi comments bane a video da nayi baki gaya min komai ba”. Da sauri tace. “Yauwa kama tuna min”. Ta ƙare maganar tana dariya tare da kallon Aunty Hauwa dake kallonta cike da alamun nazari. Sassayan ajiyan zuciya ya fesar, cike da jin daɗin ya fara sauƙar da damuwar zuciyarta yace. “Uhmmmmm ina jinki?”. A hankali ta ɗan sauƙe glass ɗin motar ta, dai-dai lokacin da suka iso Welcome to Yola, jami'n tsaron dake bisa hanyar ne ya ɗan leƙa ciki kana ya bata hanya cikin sakin sassayan numfashi tace. “Uhmmm ai jiya, kaɗan ya hana in kiraki dare-daren in gayama comment ɗin wata, to sai na tuna yanzufa kana da mata, kada taji haushina, gashi ka hanani number ta ma”. Cikin son kauda mgnar yace. “Me tace a comment ɗin?”. Ɗan juyowa tayi ta kalli Aumty Hauwa da ta tsura mata idanu tamkar ta samu TV kauda kai tayi tare da cewa. “Hmmm wata ƴar Bangaladash ce, ta fara dayin introduceng ɗin kanta ne, harda bada address ɗinta, kana ta ɗaura da cewa, tana sonka, so kuma irin na aure. Nayi dariya sosaifa ganin yadda ta watso maka emojis ɗin love, Saida na gama dariya ta sai kuma naci gaba da bibiyar comments ɗin, abin al'ajabi naje naci karo da wacce tafi na yar Bangaladash ƙwazo, itama gabatar da kanta ta farayi kana tace ita yar. Jordan ce, tace tunda take a duniya bata taɓa jin son wani ɗan Adam da muryarshi ba, kamar takaba, tace, ita indai zaka aureta, ta yafe maka sadaki, ka bata haddar Suratul Yusuf da Nisa'i da baƙara, da Khaff sune madadin sadakinta”. Sai kuma ta sauƙe numfashi tare da ɗan tsagaita wa tana ƴar dariya mai sautin, da yasa Taj jin wani irin yam tsikar jikinsa na amsa amon amintaccen sautinta. Wani irin narkewa yaji jikinsa nayi lokacin da yaji tana cewa. “Nice a raina nace, Ni dai na sani, duk faɗin duniyar nan, babu wanda ya kaini jin daɗin muryarka, kasan duk yadda sautin karatunka da muryarka ke sasu nitsuwa basu kainiba”. A hankali ya buɗe ƴan lips inshi, murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Harda Muryar Dr Nafi'u Kabir Katsina, bata kai miki tawa ba”. Cikin ƙwaɓe fuska tace. “Rabani da muryar ba katsinennan, shi sai saurin fushi”. Dai-dai lokacin kuma suka iso ƙofar gidansu, dake Airport roud. A hankali ta dannan hon, cikin sauri, Baba isa ya buɗe mata Gate ɗin,. Bayan tayi parking ne, tace. “Alhamdulillah mun iso, sai anjima zamuyi waya, in gayama sauran comments ɗin”. Cikin yin ƙasa da murya yace. “Ok sai kun shiga zan kira ki haɗani da Dadeey”. Daga nan suka katse kiran a tare. Ajiyan zuciya mai nauyi Aunty Hauwa ta sauƙe, tare ɗan dafa kafaɗar Ishmah cike da yaƙini tace. “Ishmah kuyi aure mana ke da Taj.” Cikin tsananin mamaki da yafi kama da tsoro Ishmah ta zazzaro manyan idanunta tare da dafe hannun a ƙirji kana tace. “Aure Aunty Hauwa kuma aurenma da Taj, ya Salam”. Cikin yin mgnar gsky da gsky Auntu Hauwa tace. “Yess Ishmah kuyi aure da Taj. Domin kun dace da juna, kamar dan juna Allah ya halicceku, kuma kuna son juna, irin son nan da ɗaya zai iya sadaukar da farin cikin sa ga ɗan uwansa”. Da sauri ta fara jujjuya kai cikin iyakar gskyar zuciyarta da ƙwaƙwalwarta tace. “Aunty Hauwa wlh ba soyayya mukeyi da Taj ba, ba wannan mgnar a tsakaninmu, Taj his my best friend, Taj ya zame min tamkar ɗan uwana na jini, Taj abokin hiranane, abokin shawarata, aminina, abokin kukana, Aunty Hauwa ba wannan mgnar wlh”. Taɓe fuska Aunty Hauwa tayi tare da cewa. “Yaro dai yaro ne, wato Ishmah har yanzu baki girma ba, Wai tsakanin ki da Taj kike cewa ba so, to in ko hakane babu wasu masoya a duniya kenan, inma haka kuke gani to ki sauya tunani, domin inma ke haka kika ɗauka shi ba haka yake a garesa ba”. Ƴar murmushi Ishmah tayi domin bata mantaba Garkuwa ma haka tace mata. Haka kuma Aunty Maryam ma tace mata, matar yayanta Abubakar kuma ƙanwar Barrister Kamal. Cikin son fahimtar da Aunty Hauwa tace. “Shifa Taj yanzu haka matansa biyu, kin manta ɗazu muna tafiya nake baki labarin yadda aka ɗaura masa aure jiya, ga kuma wacce mahaifinsa ya aura masa wata shida baya”. Dai-dai lokacin suka iso tsakiyar gidan, suna haura barandar Aunty Hauwa tace. “Yess kin gaya min kuma na fahimci aurenma ya yarda an ɗaura da shine saboda ke, saboda tsaida kukanki ya amince da auren, ni kuma na gaya miki Taj na sonki, kuma zamu gani in muna raye”. Tana tura ƙofar Parlour Dadeeynta tace. “Nida ga Dr Nafi'u na nan,”. Sai kuma tayi saurin ƙarasawa cikin Parlour tare da zazzaro idanu... A can Ethiopia kuwa, yana katse kiran Addawa ta kafeshi da idanun, kanshi ya kauda gefe tare da ajiye wayar gefen Laylah da tuni ta ɓingire tayi bacci, da sauri ya juyi ya kalli Addawa jin tana cewa. “Afif ka auri Ishmah itace zata baka dukkan farin cikin rayuwa duniya domin itace muradin zuciyarka. Ka aureta ka haɗa da Meymey in ma, Meymey bata kyautata makaba a wurin Ishmah zaka samu dukkan kulawa, domin kana sonta tana sonka!”. Tunda ta fara mgnar yaji bugun zuciyarsa ta tsaya cak, ya gaza koda ƙefta idanunsa, Saida yaji ta dire ayane, yana wani irin fitinenne numfashi da ya maƙale mishi cikin maƙoshinsa tare da fizgo mgnar. “ni nace Miki, ina sonta? Ni nace Miki aurenta nake nema”. Murmushin girma Addawa tayi, domin tasan Taj da zurfin ciki da haƙuri gami da juriya da iya sarrafa zuciyarsa, saidai kash duk da wannan zurfin cikin karo na farko kenan a rayuwarsa da idanunsa ke kasa tayashi ɓoye sirrin zuciyarsa, sai jin abinda kakar tashi ta faɗane ya sashi juya idanunsa tare da binne abinda Addawa ke son haƙaitowa, ya lulluɓeshi da zurfin cikinsa kana yace. “ishmah aminiyatace mai cikekken aminci, bayan Irfan Imran, da Dr Abbas da Dr Amdaz ban taɓa wasu abokai a duniya ba, sai Ishmah, saura wata ɗayama aurenta da wani babban Dr da take aiki a hospital inshi Dr Nafi'u, so ki rinƙa sanin abinda zaki ke nazarta kan mutane, Ni ba komai tsakanina da ita sai aminci”. Ya ƙarashe mgnar yana mgnar zuci. “Wai toma ni, ta ina ake fara cewa mace ana sonta, ta yaya ake iya faɗar?”. Kuwa Addawa kai ta jinjina tare da cewa. “Uhmmmmm”. Sai kuma ta miƙe ta shiga kitchen ɗinta domin ta sani muddin tasa Zulaihat ƴar ƙaninta, ta kawo mishi wani abu to bazaici komai ba. Haka yasa ta ɗauko mai gashin da tayi kishi, tare da fruits. Nigeria Cike da tsananin jin daɗi Ishmah ta rungume Dadeey data samu zaune a tsakiyar ƙanennenta. Da kuma ƴaƴanta cikin murmushi itama ta ruggume Ishmah tare da cewa. “Allah sarki Boɗɗi na, kina can kina yawon nemo min magani ko, Kinga kafin ki dawo Allah ya sauƙaƙamin”. Murmushin mai tafe da hawaye tayi tare da kallon Aunty Hauwa da ita ta ruggumeta ta gefe, sai kuma ta juya ta kalli Ummominta wanda sun kai 7 duk ƙannen Dadeey ce, sai ɗaya ce yayarta. Sai kuma Uncle Ali da Uncle Nasir wanda shine ɗan farinsu sai Hajia Aysha da ita ke binshi, sai kuma Dadeey ita kuma Aunty Hauwa ke Binta, saura dai kab ƙannen Dadeey ne, jin jinkinta ya tashi ne yasa, duk suka zo harda ƴaƴansu aurarru. Sai kuma ta kalli gefen ɗaya kuma ƴaƴanta babban dan farin Dadeey kenan Yah Muhammad, sai Yah Abubakar, sai kuma, sai Khadijah ƙanwarta mai Binta wacce a Gombe take aure, sai Adam kana Hafsat sai Hamisu sai kuma autarsu Rahama duk sunyi zobe sun sa Dadeey a tsakiya, kowa da irin kulawar da yake bata. Uncle Nasir ne ya ɗan yi gyaran murya tare da cewa. “Ishmah babu abinda zamu ce miki sai dai muce Allah ya baki ladan jinyar mahaifiyar ki, mu kuma ƴar uwarmu, tare da yin fatan Allah ya baki mijin aure na alkhairi mai riƙeki da amana da gskya da tausayawa”. Cikin sanyi tace. “Amin Yah Allah Uncle Nasir, sai kuma duk sauran umomin nata suka sukayi ta mata addu'a. Ƴah Muhammad ɗinta kuwa cikin sanyin murya cike da rauni yace. “Dan rashin auren Ishmah shine ƙololuwar damuwata, sai yanzu na fahimci cewa rashin auren nata ya zama dalilin samun nitsuwarmu wurin jinyar Dadeey domin da ace tana da aure da wuya mijinta ya barta tayi wannan watannin ko ince shakaru a gida da sunan tana jinyar mahaifiyar mu, Amman gashi yanzu ko su Khadijah mata ba sai tazoba, bare mu maza.” Kai kawai ta sunkuyar tare da fara fito da magungunan Dadeey tana shafa mata a sawunta da hannunta. Da sauri Rahma ta amsa tare da cewa. “Yau dai tunda munzo bari mu karɓeki muma mu samu ladan.” Hajia Aisha kuwa yayar Dadeey fruits take ta bata tana ci suna hira. Da sauri Ishmah ta amsa kiran Taj da ya shigo, tare da cewa. “Taj jikin Dadeey da sauƙi sosai, gata muna hira”. Cikin jin daɗi yace. “Bata waya”. Ya faɗa yana kallon yadda Abu Hashim draving ji yake kamar ya amshi tuƙin. Amsa Dadeey tayi tare da cewa. “Assalamu Alaikum Tajuddeen”. Cikin girmamawa yace. “Na'am Dadeey'nmu ya jiki?”. Tana ɗan gyara zamanta tace. “Alhamdulillah Tajuddeen jiki da sauƙi, sosai ma yanzu kam banjin komai ma, sai mutumiyar ka da idonta ke kumbure yayi jazir saboda kuka, dan Allah kayi mata nasiha tasan cewa fa, al'ƙwarin Ubangiji tabbatacce ne, kukantan nan bazai hana komai ba, ta koyi juriya, itace fa babba a mata, kaga daga wurinta ya kamata ƙannenta su samu ƙarfin guiwa, Amman da zaran jikina ya tashi sai tayi ta kuka”. Cikin sanyi yace. “In sha Allah zan yi mata mgna Dadeey kuma zata daina. Allah ya ƙara Miki lfy mai amfani”. Murmushi jin daɗi tayi tare da cewa. “Amin Amin Ameeeeeeeen Ya rabbil izzati, Tajuddeen ngd matuƙa, Allah yayi muku albarka, ka rinƙa ƙarfafa mata guiwa ka hanata kuka”. Cikin jin daɗi yace. “Amin Yah Allah”. Ya ƙare maganar da tare da nufar gidansu. Abu Hashim nayin parking Laylah tayi cikin gida shi kuwa masallacin ya wuce saboda la'asar tayi. Bayan sun idar da salla sun dawo cikin gida. Zaune yake gaban Malam tare da fara yi mishi masaj, cikin kula so Malam yace. “Kafa san in baka gari burinka kake, cikiwa wato aikin pilot, in kuma kana gari inajin dadin inji kana TAJMUH Hospital, kana cika min nawa burin na zamanka cikekken likita, domin tun a kan Hafiz nake da burin ɗana ya zama likita Amman haka bai samuba, hakama Yusuf da sulaiman da Abduraham dukkansu dai sai a kanka Allah ya cikan burina.” Cike da tsananin girmamawa da tarin irin biyayyarnan da kansa son ɗa ya fifita a zuciyar iyayensa sama da ƴan uwansa yace. “In sha Allah ranar Monday A Tajmuh hospital zan wuni”. Dai-dai lokacin Mom Amal da Aryan suka shigo, Wani mugun kallo Aryan ke bin Taj dashi saboda ganin yadda Malam ya wani haɗa kansa da na Taj ɗin har kamar zai kai bakinsa kan kunnen Taj. Mom kuwa cikin iya makirci tace. “Babanmu na kanmu Afif dottijon mai halin daddataku, kaine karaminsu kaine kuma babbansu. Tunda kai ne uban masu gida”. Ido ya ɗan ɗago tare da ɗan kallonta a fakaice, sai kuma yace. “Barka da yamma Mom”. Fuska cike da dariyar baka bana zuci ba tace. “Alhamdulillah Afif ya surkarmu”. A takaice yace. “Alhamdulillah”. Shi kuwa Malam hannunsa ya miƙa ya kamo na Aryan tare da cewa. “Matso kusa dani mana”. Kwaɓe fuska yayi kana ya ɗan zauna kusa dashi. Nan dai suka kasa suka tsare. Ganin haka yasa ya ɗan kalli Malam tare tausasa murya yace. “Yah Abana”. Murmushin jin daɗi sunan da Taj ɗin kaɗai ke kiransa da sunan a duniya yayi kana yace. “Na'am Abbana zaka tafi wurin Ummeynka ko”. Kai ya gyaɗa mishi cikin alamun neman izini. Kanshi ya ɗan shafa kana yace. “To ka gaida min Meymey in ka koma ko Abbana”. Cikin sanyi yace. “In sha Allah”. Daga nan ya fito. Cike da kulawa Ummey ke ce mishi. “Babana yaushe ne zakayi tafiya, ko ka ɗan samu hutune?”. Kai ya ɗan jujjuya alamun a'a, ganin yadda ta tsareshi da ido alamun neman ƙarin bayani ne ya sashi ɗan motsa lips inshi a hankali yace. “Next week ma, zan wuce Mexico City amman kwana ɗaya zamuyi acan zan wuce Istanbul to acan kuma kwana biyu zamuyi zan juyo da Passingers ɗin mu na Ethiopia”. Cikin jinjina zirga-zirga da yake sha tace. “Allah ya baka Sa'a ya kaiku lfy ya dawo mana daku lfy”. “Amin ya Allah Yah Ummeyna”. Ya amsa cike da alamun zazzafan shaƙuwarson uwa da ɗanta. Sai kuma suka kalli Zakiya data zauna gefenshi tare da cewa. “Dan Uncle Taj yanzu ƙasashe nawa kaje a duniyar nan?”. Kanshi ya ɗan jujjuya mata, alamun shima bai san adadin su ba. Sai kuma ya ɗan kishingiɗa jikin kujerar tare da ɗaura kansa bisan cinyar Ummeynshi lokaci ɗaya kuwa bacci yayi awon gaba dashi dan, jiya da dare bai samu isasshen baccinba. Zakiya kuwa hannun Laylah taja tare da cewa. “Mu tafi Saloon, dan na lura Uncle Taj shine auta ba niba”. Ita dai Ummey murmushi kawai tayi. Fahimtar baiyi baccin ba yasa tai ta shafa kansa, dan ta fahimci yana da damuwa zurfin ciki ya hanasa bayyana dama kuwa ta sani bazai bayyana ɗinba. A can gidansa kuwa, Meymey ce, kwance bisa gadon ta, riƙe da wayarta tana mgna da Dr Zakariyya cikin ƙarfafamishi guiwa tace. “Zamuyi fa, komai zai tafi dai-dai kada ka tsorita, bazai taɓa fitowa yayi inkarin wanke kanshi ba, kuma in ma yayi inkari ai muna da manyan hujjojin da zamu kafa”. Cikin shakku Dr Zakariyya yace. “Hummm kinfa san shima Doctor ne daya fini, matakin sanima, tunda shi a ƙarƙashin sa ma, likitoci sama da 8 ke aiki a Hospital inshi”. Da sauri tace. “Kada ka damu”. Daga nan taci gaba da ɗaurashi bisa hanyar. Gab da Magrib Halima da taje gidan Rashida ta dawo, cikin mamaki tace. “Kai Ummey harda zama ki nitsu yana wani bacci a jikinki, ina matarsa da zai zo ya ɗale mana cinyar uwa”. Da sauri Ummey tace. “Toh ai uwar tasa ce shi kaɗai, ku kam duk na bawa Addawa na ku”. Dariyar Halima ne ta tashesa, kuma dai-dai lokacin aka kira sallan Magrib. Bayan an idar da sallan, Isha a nan a Parlour Ummey sukayi Dinner shida Laylah kana suka koma gida. A Parlour ya sameta zaune tana waya da Abbanta Uncle Jibirin kenan ya fahimci haka ne jin tana cewa. “Eh Abba na lfy Lau muke, gashi ma yanzu ya dawo gidan, Ummey ya tafi ya barni gidan shiru, gashi in baya nan gidan ba daɗi”. sai kuma ta nufoshi tare da cewa. “My Love ka dawo”. Ta ƙare faɗin hakan tana hararan gefen TV. Da sauri Uncle Jibirin ya kashe wayar. Ita kuwa Murmushi mai cike da makirci tayi, sai kuma tayi saurin sunkuyar da kanta lokacin da ta ɗago da niyan kallonsa, bazata taɓa iya jure ganin kwayar idanunsa ba, domin suna da wani haiba mai sa makirai rusunar da kai, Fuskantar sa Kuma nasa zuciyar makirai karaya. Ɗakin Laylah ya wuce, bisa gadon ya kwantar da ita, tare da yi mata tofi kana ya rufeta da blanket sannan ya fita ya nufi ɗakinsa. Ita kuwa Meymey ƙofar Laylah ta zubawa ido tana Murmushin. Yau Monday tushen aikin. A hankali Abu Hashim yayi parking cikin harabar wani tamfatsetsen asibiti na gani na alfarmar, irin asibitin nanne mai tsari na alfarmar ba matsin ko cunkoso. Daga can sama tsololuwa an rubuta. *TAJMUH CONSOLATION HOSPITAL* da manyan baƙi. Harabar asibitin yalwataccen ne parking spaces ɗin nasu, mai faɗi, wanda a ƙalla zai iya ɗaukan motoci 15, zuwa 20 ba tare da wata ta matsi wata, ko ta gogi wataba. Sai kuma doguwar katanga da tayiwa asibitin garkuwa, yayinda bishiyoyin dogon yaro ke zagaye dashi iyakar ganinka, sai kuma ƙasansu wasu ƴan dagwai-dagwai ɗin bishiyoyin dabino ne guntaye, masu masifar ƴaƴa da ɗan karen zaƙi, gasu ringiz gwanin ban sha'awa. Sai daga ƙasan farfajiyar kuma, tsirran flowers ne masu ƙamshi ke zagaye da lungu da saƙo. Daga saman Benin dake fuskantar gate ɗin kuma an rubuta. Admin Maternity and Surgery block. Gaba ɗaya fuska wurin marafen Glass ne mai garai-garai wanda zaka iya ganin kanka ras a ciki. A dai-dai gaban wurin Abu Hashim yayi parking, yayinda Mai gadi da masu bawa flowers ruwa, sai kuma masu cliners dake ƴan share-share da goge-goge wanda tuni sun kammala aiyunkasu domin da dama moppa suke wankewa, masu tura dozbin na turawa. Da sauri Maigadin ya buɗe masa marfin motar, shi kuwa Abu Hashim fitowa yayi hannunsa riƙe da briefcase ɗin uban gidan nashi, tare da ɗan tsayawa gefen ƙofar, sukayi jim suna jiran fitowarsa. Yess in da sabo ai sun saba sun san halin sanyinsa. Yakan iya kai 3 minute zaune a cikin motar duk da yasan sun iso, a da can baya ma, bare yau a kuma cikin yan kwana kin nan. Dai-dai lokacin kuma a can cikin Reception ɗin nasu, wata Nurse ce ta shiga cikin Pharmacy dinsu, tare da kallon wacce ta samu a ciki, tare da juyawa ta kalli bayanta sai kuma tace. “Hajara albishirinki dama Dr Taj a cikin hospital nan”. Cikin rumtse idanunta Hajara ta ɗan ɗaura rafin hannunta bisa ƙirjinta dake, jin yadda Heart ɗinta ke beating so fast, sai kuma ta buɗe idanunta tare da cewa. “Zuciyata ta rigaki sanarmin”. Murmushin wacce ta shigo ɗin tayi tare da cewa. “Wlh kina bani tausayi, sai dai kuma wasu lokutan in naga Dr Taj ko naji Voice ɗinsa nakan ce dole, ƴan mata su rikice su ɗiwauce da sonshi, saboda ya kai a soshi, haibarsa kuma da nagartasa ta isa ta hana ƴan matan sabun damar isar da sonsu, toh suna da suke da aure ai sai dan kariyar Allah da darajar aurene yake hana shaiɗan samun damar farma zuƙatansu. Da sauri ta fito daga Pharmacy ɗin, ta koma Registry, inda nanne wurin aikinta. Ita kuwa Hajara ta gyara zamanta tayi, dai-dai lokacin kuma Dr Abbas ya fito daga Consultings room 1, ganinsa yasa duk suka nitsu. Patients insu wanda a ƙalla sun kai 9 ya kalla tare da yi musu, ya masu jiki. Kana ya wuce ya nufi hanyar fita. A bakin ƙofar fita Reception ɗin ya tsaya tare da zuwa aminin nasa idanu yana mai sakin murmushi. Cikin da nitsuwa ya fito daga cikin motar cikin shigar suit Morning sky color masu masifar kyau, da sheƙi, yayinda long sleeve shirt dake ciki ya ƙara ƙawata shigar tasa, net ɗin dake zagaye da wuyanshi shima maroon color sai ratsin Morning sky, sai kuma Half cover shoe dake saeunsa, na kamfanin Gucci shima maroon color. Wani irin ni'imtaccen ƙanshin mai masifar daɗi yake bazawa, na turaren kamanin Gucci, intense Oud. sai ɗan siririn glass farin ƙal, dake manne kam kekkyawar fuskarsa da saje yayi mata ƙawanya, ya ƙara mata haiba da kamala. Kusan duk a tare Ƙananun ma'aikatan nasa sukayi mishi zobe, suna kwasar gaisuwa kamar yadda ya saba haka ya fara, amsawa yana mai jinjina musu da basu ƙarfin guiwa yake cewa. “Aikin ku yanayin kyau, manyan ma'aikatana”. Yayi mgnar da iya kar mutumtaka tare da ɗan jujjuya ƙwayar idanunsa ganin ko ina na cikin Hospital ɗin yayi fes-fes gwanin kyau. Maigadin ne yace. “Sir kar Doctors su Doctors inmu suce kana bamu matsayinsu fa”. Kai ya ɗan jinjina tare da cewa. “Matsayin ku ya ɗara na Doctors and Nurse's ai, domin in babu ku a asibitin, ƙazanta zata sa babu Dr da zai yarda yayi aiki anan, bare kuma patients su zo”. Cikin jin daɗin karramasun da yake yi, suka rinƙa godiya kana suka juya kowa ya koma bakin aikinsa. Shi kuwa Taj juyawa yayi ya ɗan fuskanci gefen gabas, inda wani tamfatsen gini na musamman yake shimfide daga sama an rubuta Reception. Da manyan baƙi, Cikin sauƙe numfashi ya nufi ƙofar shigan. Abu Hashim na biye dashi a baya, riƙe da briefcase inashi. Murmushin mai nuna cikar jin daɗin Dr Abbas yayi tare da cewa... Ba editing kunsha typing errors. By *GARKUWAR MARUBUTA* [1/8, 5:26 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 7* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin INDA RAI na kiɗine yanzu free pages ne mukeyi ki biya ki karanta cikin aminci da salama. 1k ne kacal 0661110170 Gtbank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number zaki turo min shaidar biyanki 09097853276. Mutanen kasar Niger kuma 1000fc ne zaku biya jaka ɗaya ne kacal zaku tura +22790899076 Ta wurin Mommy* Yau tallana na nakune Mutanen Ƙasar Niger. More especially, ƴan Niamey ko masu dangi anan ko ƙawa ko abokin, da in na tura muku kaya can zaki samu mai amsa Miki shi yasa Miki shi a motar garinku, inma kuma ace duk ma baki da mai amsa Miki, Driver da zai taho da kayanki daga Sokoton Nigeria, zuwa Niamey Niger zai sa Miki shi a motar state da kike. Akwai kuma Garabasa ta musamman wacce takuce, step ɗin kayana akwai manya set akwai kuma ƙanana, domin banafa barin Customer tazo da kuɗinta su koma, ga farashin su biyo kiji. Manyan set ɗin daga haka arba'in, jaka hamsin, jaka settin, jaka saba'in, jaka tamanin, sune manya a yanzu saboda kuɗinki sun yi sama sunfi naira, Amman in naira ta kuma hawa ta fi nakun zai zama manyan set ɗin daga jaka 50, 60, 70, 80, 90, 100, ƙananan set ɗin kuma yanzu daga jaka talatin ne, haka ashirin da biyar, jaka ashirin, jaka sha biyar, jaka goma, sai kaja takwas banayin haɗin ƙasa da jaka takwas, sai kwanon Ƙasaitacciyar mace shi jaka biyar ne. A yanzufa kenan, in kuma Naira tayi kunnen doki da kuɗinki to ƙanan set ɗin Daga jaka 40k 35k 30k 25k 20k 15k 10k sai kwanon Ƙasaitacciyar mace 7k idan kin sayi kayana ni free Delivery ne Adamawa to Sokoto ke kuma sai kiji da sauran. Fara samun tangarda, sai kuma tayi shiru tana sauraron tausasan kalamansa. “Duk mijin da kikaga, ya nemi aurenki daga bisani ya janye, toh dama can Allah bai hukunta zamowarsa mijinkiba, ke muminace, kuma saliha, tsarkakekkeya dan haka, ki kwantar da hankalinki, inada kekkyawan yaƙinin Ubangijin talikai da kika tsare mutuncin kakin domin sa, baki saɓamasa, yayi Miki tanadi da miji mumini, salihi mai sonki, tamkar ransa, mai ji da gamsuwa cewa in babu ke cikin rayuwarsa bazata yi armashi ba, yana nan tafe gareki zai kuma iso a duk lokacin da Ubangiji ya ƙaddarta faruwar hakan, so please kada kiyi kuka ki zubda min raunatattun hawayen akan Dr Nafi'u, ki adanasu domin Taj ɗinki baya son zubarsu, kiji ko Ishmah Boɗdin Dadeey”. Sassayan numfashi mai cike da korar damuwar dake ranta ta fesar kana a hankali tace. “Taj yau kwana uku fa, kenan Dr Nafi'u baya kirana sai in ni na kiranshi, yace min muje muyi gwajin Genotype naje munyi kuma yaƙi ya gaya min Result ɗin, sannan yazo ya daina kirana, ya zanyi in banyi kuka ba kuma ni dai nasan bani da matsalar komai. Dadeey nama kanta abin ya bata tsoro ɗazu sai cemin tayi Allah yasa tana da rabon ganin na sakeyin aure”. A hankali ya ɗan kalli far-fajiyar gidan nasu lokacin da Abu Hashim yayi parking. Cikin sanyi ya rumtse idanunsa da ƙarfi domin ji yake zuciyarsa na hankaɗo abinda ke cikinta tsawon shekaru yana tahowa kan harshensa. Saboda jin abinda Ishmah ke faɗi. “Taj 7 yaers fa kenan yanzu har za'a shiga na 8 Taj banyi aureba, Abba na kanshi abin na damunsa Taj”. Ta ƙira sunansa cikin raunatacciyar murya da alamun zubda hawayen wanda hakan ya sashi ƙara jingina da car seat ɗin tare da cewa. “Na'am Ishmah, menene? Gaya min?”. Murya a sanyaye tace. “Taj ina son inyi sure ko dan farin ciki Dadeey da Abba na, inason inyi aure ko dan samun nitsuwar zuƙatansu”. A tausashe yace. “Zakiyi aure Ishmah zakiyi auren da zasuji daɗinsa, kinji ki daina kuka, yanzu muje kirakani in sallami Yah Abana da Ummey ko, zan wuce Airport ƙarfe goma zantashi”. Tana mai share hawayenta tace. “Toh”. Ba tare da ya katse kiranba yasa wayar a aljihun ƙirjin jallabiyarsa kana ya fito. Zaune ya samu Ummeynshi da Yah Abana a pravet Parlour inshi kasan cewar yau Ummeeyshi ce da girki. Tea Ummey ta haɗa mishi tare da miƙa mishi. Amsar mug ɗin yayi tare da ɗan ƙara matsota kusa da Malam, ɗin kana ya ɗan gyara zamansa ya tankwashe sawunsa, yana mai fuskantar su, murya cike da girmamawa yace. “Yah Abana”. Murmushin Ummey tayi tare da zuba musu ido, Allah ya sani Taj shine farin cikinta mijinta kuma shine duniyar ta, bata jin zata iya rayuwa ba ɗayansu a rayuwarta ta kuma samu farin ciki, ita kanta tasan biyayyar Taj da Alkunyarsa da haƙurinsa ne ke ƙara zuzuta soyayyarsa a zuciyar mahaifin nasa da har yake gaza iya ɓoyewa. Lumshe idanunta tayi ganin shima malam ya ɗan gyara zamansa tare da ɗan ronƙofowa ya matso da kansa kusa da fuskar Taj ɗin kana yace. “Na'am Abbana ya akayi?” Murmushin Ishmah tayi tana mai jinjina son dake tsakanin uba da ɗansa, sai kuma ta kuma sakin murmushi mai sauti jin Muryar Ummeeyshi na cewa. “Malam irin wannan kasa da murya da keɓe kunne, duk nice ake ɓoye abin da ake son tattaunawar”. Lunshe ido Taj yayi tare da ɗan manna kanshi da guiwowinta kana yace. “Ummeey na me zamu ɓoye Miki, kecefa muhalit sha'eyd na ko wacce mgnar da zamuyi”. Sai kuma ya kalli Malam ɗin dake shafa kansa. Hannunsa na dama ya ɗaura kan hannun mahaifin nasa yana mai asawa da Amin jin addu'o'in da yake jero masa. Dai-dai lokacin kuma zaratan ƴaƴansa suka shigo Parlour a jere domin zuwa yi mishi sallamar zasu tafi wuraren aikinsa. Kusan a jere suka shigo, cike da son zaratan yaran nasa wanda tuni wasu irin Yah Hafiz Yah Sulaiman, Yah Yusuf, Yah Abduraham, duk sun zauna a gabanshi irin zaman nan na neman albarkar iyaye, Cikin kulawa Ummeey ta kalli Yah Aryan da Kabir dake tsaye tace. “Bismillah Aryan Autan Kabir ku zauna mana”. Wani irin kisataccen kallo Aryan ya jefa wa Taj tare da kwaɓe fuska kana yace. “Uhmmm ai ga auta kam ana sa mishi al'barka na musamman”. Ya ƙarashe mgnar yana ɗan tauna lip inshi na ƙasa saboda azabtar suya da zuciyarsa keyi. Kabir kuwa sunkuyowa yayi ya zauna jin Malam ya jawo hannunsa ya jawosa zaune, ganin haka ne yasa Aryan ɗin ma zama. Ummeey kuwa kasake tayi tana, nazartar kalaman Aryan tana haɗesu da irin kallon da yake bin Taj dashi tana ƙara haɗesu a mizani ɗaya da kalaman Mom Amal a lokuta da dama. Shi kuwa Taj hannu ya rinƙa bawa yayun nasa tare da gaidasu. Cike da so suke amsawa, daga ƙarshe ya miƙawa Aryan hannun kauda kansa yayi tare da amsa gaisuwar ba tare da ya bashi hannun ba. “Uhmmm”. Ummeeyshi ta saki wani ɓoyeyyen numfashi ganin yadda Kabir ma ke bin Taj ɗin da bahagon kallo. Sai kuma tayi murmushi ganin Yah Hafiz ya ɗaura hannunsa bisa kan Taj ɗin tare da cewa. “Baban Malam naji yaranka Imran da Arfa sunce yau zaka tashi zuwa Mexico City, sunanta murnar zasuga Uncle Afif.” Murmushin yayi tare da sunkuyar da kansa. Aryan kuma tsuke fuska yayi shi ya tsani yadda aketa maimaitawa cewa Taj ne ya ɗauki nauyin karatun ɗansa. Ai ga Yusuf ma Taj ɗin ne ya ɗauki nauyin karatun ɗansa Malam ƙarami yana karatu a kan ball sam ba'a zuzutashi kamar nasu, kuma shi ba roƙa yayi ba shima yana da arziƙin da zai iya karantar da ɗansa”. Yah Sulaiman ne ya ɗan kalli Taj ɗin tare da cewa. “Jiya Inti ke cemin Abbu Uncle Afif ya zamon jiya da yamma.” sai kuma ya ɗan kalli yan uwan nasa da mahaifinsu kana yaci gaba da cewa. “Waifa cemin take Abbu duk Uncle Afif ya fiku sonmu, in dai yazo gari to sai ya ziyarcemu yazo kuma yace min zan koma makaranta”. Sai kuma yayi Murmushin jin Yusuf na cewa. “Haka tace min kwanaki wai ai Abbunta kam ma bai taɓa zuwa gida taɓa. Muma sai haihuwanta ne muka je”. Cike da jin daɗi Sulaiman yace. “Toh dan Allah Malam inje ince me,”. Dariya sukayi baki ɗayansu banda Aryan da Kabir Abduraham kuwa cikin sanyi yace. “Yara da daɗi”. Da sauri Taj yace. “In sha Allah kaima zaka haihu Yah Abduraham”. Murmushin yayi tare da cewa. “Allah yasa haka”. Sai kuma malam yayi gyaran murya tare da fuskantarsu da kyau kana tay fara jero musu addu'o'i ɗaya bayan ɗaya. Suna amsawa da Amin Amin. Da sauri Taj ya ɗan kalli Malam ɗin sabida ganin har 8 ta kusa cika. Cikin sanyi yace. “Yauwa Yah Abana batun asibitin nan ne na Qatar da nace maka an tallata min, shine nake so, a tayani da addu'a idan sayansa alkhairi ne Allah ya tabbatar idan kuma ba alkhairi Allah ya musanya min da abin da yafi alkhairi”. Kusan a tare Malam ɗin da yayunsa duk sukayi ta mishi fatan al'khairi. Harda Aryan da Kabir wanda ganin idon Malam na kansu ne yasasu yin fatan alkhairi. Daga nan duk suka fita. Shi kuwa Taj a hankali ya ƙara matsowa tsakiyan iyayen nasa, a tare suka ɗaura hannunsu a kanshi suka haɗa bakin. “Allha ya kaika lfy, ya dawo da kai lfy, ya al'barkaci rayuwarka ya azurtaka da yara na gari masu yi maka biyayya fiye da yadda kakeyi mana, ya azurta yaranka da irin haƙurinka da kawacinka”. Yana mai lumshe ido yake amsawa da. “Amin Amin”. Sai kuma ya kalli Ummeynshi jin tana cewa. “Sai dai bana fatan yaranka su ɗauki zurfin cikinka domin zasuyi ta cutuwa. Da kuma ɗayan halin bana so su ɗauka”. Sunkuyar da kanshi yayi ƙasa, malam kuwa cikin kula yace. “Ni nafi tsoron ɗaya halin nashi nema, don zurfin cikinsa bai bani tsoro kamar ɗayan”. Ya fahimci cewa faɗa da nasiha sukeyi mishi cikin son nuna suna ƙin wannan halin nashi da shi bai san ya zaiyi ya canza kansa ba. Yadda in an ƙureshi a abu yayi riƙo sakewa nayin wuya” Ita kuwa Ishmah cikin sanyi ta fesar da numfashi, tana nazartar wannan halin da suke faɗin. Sosai sukayi mishi nasiha kana ya fita suka tafi. “Baba Malam”. Shine sunan da Ishmah ta kira shi dashi lokacin da ya ƙara wayar a kunne. “Na'am Maman Abba”. Ya faɗa, tare da kallon Abu Hashim yace. “Ka hanzarta fa”. Sai kuma ya ɗan gyara zamansa tare da cewa. “Muje Airport ko?”. Cikin sauƙe numfashi tace. “Afwan ai na iso har na shirya na taho Hospital inmu, Khalid ma ya wuce school yau da sassafe yazo wai yazo duba Dadeey da jiki shine ya samemu a haka har ya kai maka rahoto”. “Ok to ba matsala sai na sauƙa a Mexico zan kiraki”. Daga nan sukayi sallama Takwas da rabi dai ta samesu a cikin. Addis Ababa bole intranational Airport. Yana isa escorts in shi, na biye dashi a baya, na gefen damanshi ne ya amshi briefcase inshi daga hannun Abu Hashim, daga nan shi ya juya ya koma gida. Side ɗin da ake tantance lfyar pilots and Hostess ɗin su ne ya wuce. Shigarsa da kamar 26 minutes ya fito, riƙe da wasu files bisa dukkan alamun rahoton lfyar Hostess ɗin da zai tashi da sune, kasan cersa pilot kuma likita shiyasa yake samun wannan damar. Wani ɗakin ya shiga mai masifar kyau da tsaruwa wanda yake da girma da faɗi ga haske kai kace da rana ne, Ƴan matan Hostess ɗin sune a jere kusan su goma biyar a gefen dama biyar a gefen hagu. Sai kuma wani mutum a gefe bisa alama shima pilot ne. Hostess ɗin suna tsayene tamkar waɗanda aka dasa, a jere suke gwanin ban sha'awa. Kusan tsawonsu duk dai-dai ne haka ƴar ƙibarsu. 8 daga cikinsu fararene ƙal irin farin Ethiopia's Gerls sai kuma biyu daga ciki Chocolate collor ne mai ɗan duhu. 8 daga cikin sanye suke da Uniform insu Nevy blue, mai masifar kyau, riga da sket ne, sai hulunan da suka kafa a kawunansu, Sai biyu daga cikinsu kuma suma riga da sket ne sai dai kalar nasu farine kuma ya ɗanfi na sauran ɗan faɗi da tsawo, kana su akwai mayafi, ƙasan sket ɗin da mayafin an mishi ado da zare Nevy blue. Yayinda duk sawunsu ke sanye da cover shoe mai masifar tsini da tudu. Bisa alamu biyun nan masu mayafi su musulmai ne. Sai wani irin fitinenne ƙamshi suke bazawa, tamkar anyi barin turare. A hankali yake taku mai cike da kamala haiba gamida kwarji. Jin wayarsa na Vibration ne ya ɗan sashi zaro wayar da niyar katsewa ganin. Sunan dake yawo a fuskar wayarne ya sashi amsawa, tare da manna wayar a kunnensa ya maƙale ta da kafaɗarsa. Sai kuma ya tsuke fuska yayi kici-kici da ita, domin ya tsanin irin masifeffen kallon nan da Agnes Samuel keyi mishi waccan itace ta biyu a layin hagunsa. “Hummm”. Yace can ƙasan maƙoshinsa jin Ishmah na cewa. “Dama na kira inji ko kun tashi ne?”. Sai kuma tayi shiru jin ya ɗanyi gyaran murya cikin dakekkiyar murya mai cike da isa yace. “Na lura wasu daga cikinku, ba aikin bane a gabanku, kallo nane yake kawosu”. Da sauri duk sukayi ƙasa da kai. Ishmah kuwa Murmushi tayi fahimtarta yana nufin da Hostess ɗinsu ne, shiyasa ta gyara zamanta tare da maƙale wayar. Shi kuwa Taj a hankali yake taku har ya iso tsakiyarsu. Pilot ɗin nan kuwa Murmushi mai ɗan sauti yayi, sai kuma yayi saurin sunkuyar da kansa ganin kallon da Taj ɗin ya jefa masa. “Ganan Result's in gwajin da akayi muku, dan sanin ingamcin lafiyarku, Abin takaici, ba a sami meku da cutar da Allah kan ɗorawa bawa ba, sai fitinar tsiya da aka samu a cikin wasunku, wanda suka ɗaurawa kansu. Ni kuwa bazan iya tafiya da mace mai irin wannan matsalar ba, Bisa wannan dalilin ne Agnes Samuel bazanyi tafiyar nan da keba, ki koma gida ki gayawa iyayenki abinda kike so su miki sure. Sai ke kuma Jannifer kema bazamu tashi da ke ba. Ki huta sabido ba aikin bane a gabanku”. Wani irin kallon ƙasa-ƙasa mai cike da tsananin flenings da son kusanci da tsarkakken fatar Taj ɗin da shine muradinsu, sukayi ƙasa da kai. Domin sun san mgnar sa, ɗaya ce in ya faɗa ba fashi more especially irin yau yadda ya tsuke fuska da watsa musu kallon tsanan da yasa suka gaza haɗa ido dashi. Sanin basuma isa suyi musu ko inkari dashi bane yasa sukayi cib kamar gumakai sai tsananin takaicin soko sunansu da yayi daga tafiyar. Dai-dai lokacin kuma wasu ƴan mata biyu masu shiga irin na musulman cikinsu suka shigo. Suna shiga yayiwa Agnes da Jennifer nuni da hanyar fita. Cikin tsananin son da Agnes keyi mishi da zafin sha'awarsa dake nuƙurƙusan zuƙatansu suka haɗa baki wurin cewa. “Thanks”. Gashi dai sokesu yayi Amman dole suyi mishi godiya, Kauda kanshi yayi kamar bai jisuba, hakanne ya basu damar zuba mishi ido haɗi da mgnar zuci. “Shi Taj namiji ne irin wanda duk macen da tasan maza da ban-da ban zatayi buri da fatan mallakarsa, domin ƙwayar idanunsa kaɗai na iya bayyana suffarsa ta zaraceccen namiji mai cikar sura uba uba gashi dogo, kana gashi bashi da wawan jikin da zai iya tauye Taj ɗin, kana ga shafeffen cikin dake bayyana guru-gurun murɗuwa ta cikin tattausar jallabiyarsa dake manne da cikinsa wanda murɗewar cikin da lafewarsa ne zai ƙara bayyana isar Taj ɗinsa. Wani yawun sha'awa Jennifer ta haɗiye muƙut lokacin da idanunta suka sauƙa kan lips inshi masu kama da kunnen fure. Sai kuma sukayi saurin ficewa tare da jan ƙofar. Tsaki mai sauti yaja tare da fara zirya yana mai faɗin. “Duk wacce tasan kallona ne ya kawota, ta faɗa tun wuri domin ko munje Mexico naga ƴarinya na min kallon maita acan zan watsar da ita, in wuce Turkey. An ɗaukeku aikine domin kula da Passingers ɗinmu da sauran ayyukan da wajibinku ne, dan haka ku kiyayeni, kun fahimta.” Yess sir suka haɗa baki wurin faɗa. Da hannunsa yayi musu alamun su tafi su fara aikinsu. Cike da nitsuwa suka nufi hanyar fita, suna irin takunsu na tada fitina. Pilot Sassy kuwa ɗaya hanyar yabi ya fita. Shima Taj a hankali yabi bayan Sassy. Ishmah kuwa murmushi tayi cike da shaƙuwarsu tace. “Taj meyasa ka soke tafiya dasu?”. Sassayan numfashi ya fesar tare da yin mgn murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Yara gaba ɗaya jarabar son maza ya hanasu nitsuwa, sannan ina shiga suna bina da kallo tamkar kura yaga ɗanyen nama”. Da sauri tace. “To shine sai ka korasu”. Tamkar cikin raɗa yace. “Ishmah tsoro suke bani”. Sassayan dariya mai sautin da yasashi murmushin jin daɗi tayi kana tace. “Toh tsoron me kuma, me zasuyi maka kana uban gidansu, ta ƙare maganar tana ƴar dariya mai sassayan sauti, sai kuma tayi cib jin yana cewa. “Tsoro nake kada su danneni suyi min fyaɗe”. Ya Salam da sauri ta katse kiran. Tana mai rufe idanutan da tafukan hannunta duka biyu saboda kunyarshi daya rufeta kalamar shin tazo mata a bazata don tsawon shekaru da suke tare bai taɓa yi mata ma kamancin kalmar ba. Shi kuwa Taj ido ya lumshe tare da zira wayar a aljihunsa kana ya shiga cikin jirgin. Karfe goma dai-dai jirginsu ya tashi daga Ethiopia zuwa Mexico City. Bayan kwana uku. Abpu ne tsaye gaban Ummi cikin tsananin ɓacin rai yake faɗa. “Ya za'ayi ki bar Adaya ta fita, bayan kina sane da cewa akwai igiyoyin aure a kanta, ya zaki min haka ina tubka kina warwara Hafsa, kina sanefa dan wannan yawace-yawacen da rawar da takeyi yasa na ƙudurta aniyar aurar da ita domin gudun lalacewarta”. Cikin sanyi da tarin takaici Ummi tace. “Apbun Adaya ka sani cewa, Adaya ta rainamu saboda son da muka nuna mata da tausayin maraicinta, yasa bata jin tsoron mu, ba yadda banyi da itaba kada ta fita Amman ina taƙi, sai cemin tayi ai dole ta fita, tunda wurin rihazal ɗin gasarar rawar da zasu tafi India nanda wata uku, zataje kuma itace jagorar tawagar Ethiopia, wlh har hawaye nayi Amman Adaya tayi nisa bata jin kira”. Cike da takaici Abpu ya wuce Parlour sa yana mai zubda hawayen takaici. Nigeria A hankali Dr Nafi'u ya tashi zaune tare dasa hannunshi duka biyu ya rumtse kansa a fili yace. “Im so sorry Aysha ina sonki, bana son cutar dake, in kuma na aureki dole zan raɓa miki cutar HIV dake tare dani, kuma ji nake bazan iya juran rasaki ba domin ina son mallakarki a shimfiɗata, nasan zaki jiyar dani daɗin da babu wata ƴa mace data taɓa jiyar dani, Bana son rasa ni'imar da nake ganin alamunta a jikinki. Bana kuma son cutar dake”. Sai kuma ya tashi tsaye tare da kifa kansa da jikin gini yana ganin surar jikin Ishmah nayi mishi yawo a idanunsa. Ishmah farar macece ƙal, ƴar duma-duma mai ƙirar jikin da duk wani lafiyeyyen namiji da zai ganta zanji lafiyarsa ta motsa, Tana da ɗan tsawo dai-dai misali, ƙirjinta irin ƙirjin nanne da yawan shekaru ko yawan haihuwa baya sa ya caɓɓullensu zubewa, a cike suke tib-tib gwanin ban sha'awa tamkar tsada, suke dan fari npls ɗinta kuwa irin mai masifar tsokar mazane domin a tsaye suke cas. Cikinta kuwa a lafe yake, sai hakan ya bawa Ƙugunta damar bajewa mazaunanta a sama suke, kana masu ɗan motsawane in tana tafiya. Fuskarta kuwa mai zubin o ne tana da manyan idanu farare masu lumshewa, sai hancinta dai-dai da fuskantar dan bai cika tsawoba sai ƴan siraran Pink lips inta masu masifar taushi da sheƙi kamar kunnen fure gefe duka biyu duka tana da Dimples har a tsakiyan gemunta in tana dariya yana ɗan lotsawa. Da sauri ya buɗe idanunsa tare da cewa. “Wallahi bazan iya haƙura da keba Ishmah”. Ya ƙare maganar yana tuna yadda idanunta kan sauya launi in rauninta ya motsa da sauri ya dauki rigarsa ya zura tare da surar key ɗin motarsa kana ya fito ya nufi gidansu Ishmah yana mgnar zuci. Zaune suke a Parlour Abbanta, cikin sanyi yace. “Fushi kikeyi da niko?”. Kai ta sunkuyar ƙasa tare da cewa. “Miss calls 37 nayi maka baka ɗauka ba, text message 7 ba amsa, kwana biyar kenan yau baka zoba, baka kirani ba baka bari na ganka a Hospital ba, meyasa ka zabi da ka azabtar dani da hakan?”. Cikin salon rarrashi ya zamo ƙasa ya durƙusa a gabanta tare da cewa. “Afwan kiyi haƙuri wai ni kuma nayi hakanne da in gwada ƙarfin soyayya ta a zuciyarki”. Cikin narke fuska tace. “Toh ya ka gani”. Yana murmushi yace. “Dari bisa dari, fatan dai kina lissafin cewa yau saura. Kwana 18 arenmu ko”. Cike da jin daɗi tace. “Ni da har na fara tunanin in haɗa kayanka da kuɗin sadakinka in bada a maida maka”. Cikin jujjuya kai yace. “Azubullahi banji wannan mgnar ba”. Haka dai sukaci gaba da hirar tsara bikin nasu sai kusan Magrib ya tafi. Tana dawowa Parlour Dadeey tace. “Dadeey ba Kinga Dr da bada tsoroba wai gwadani yayi”. Daddey na miƙewa tsaye tace. “Haka yace min ai yayi ta bani haƙuri”. Daga nan suka je sukayi al'wala dan sallan Magrib. Washe gari, ranar Friday Misalin ƙarfe 11 ɗaya dai-dai. Taj ne kwance bisa gadon dake cikin ɗakin binciken lafiyar pilot ɗin da zasu tashi na cikin Istanbul Ataturk Airport. Lunshe idanunsa yayi da karfi lokacin da yaji Dr na ɗan latsa saman mararsa, sai kuma ya ɗan kalleshi tare da cewa. “Kamar akwai abinda kake buƙata. Ya kamata a magance matsalar nan kafin ku tashi, don gudun kada ku tashi sama mararka ta murɗa kaga rayukan mutane zai shiga haɗari”. Yana ture hannun Dr da ya kasance ɗan asalin ƙasar Turkey ɗine a taƙaice yace. “Tun shekaru huɗu baya haka nake rayuwa, ka duba bayanan lfyata da Mexico ta tura muku kafin sauƙata, ko ka duba cikekken bayanin wannan abun da kake ganin kamar matsalace a gareri a shafin lafiyar Ethiopia's pilots ɗinmu”. Cikin sauri Dr yayi saurin juyawa kan na'urorin dake zagaye dashi ya fara dudduba wasu abubuwa cike da mamakin ganin yadda Taj ɗin nasa ke a hanzarce duk da bawai yayi irin azamar neman agaji bane Amman kuma ba a kwance yakeba, tunda gashi har a ta sama wondo suit ɗin dake jikinsa ya nuna hakan. “Haka kake rayuwa, to kayi aure mana”. Yana mai miƙewa zaune yace wannan ba matsalarka bace”. Dan Allah ya sani ya tsani wannan gwaje-gwajen jarabar tsiya da akeyi musu duk sanda zasu tashi. Daga nan ya fita, shi kuwa Dr cike da kallon mamakin irin zarrar jikin Taj ɗin yake mamaki da jinjinawa lafiyarsa, gashi kuma bisa alamu ba mazinaci bane, Domin da mazinacine ai da yace akawo mishi mace, a hankali yace. “Alhamdulillah alah ni'imatil islam”. Yasan cewa wannan ƙarfin tsarkin addinin Muslunci ne. 11:00 pm jirginsu ya tashi zuwa Ethiopia. Washe gari ranar asabar, ta kama saura kwana 15 auren Ishmah da Dr Nafi'u, Kana saura kwana 9 Taj yazo Nigeria. Ishmah ce zaune a Parlour Garkuwa, Yayinda suke magana mai mahimmanci a hankali Ishmah tace. “Nifa tsoron shan magungunan nan nake Garkuwa, saboda gani nake kar in tsuma jiki aure ya watse, abu ɗaya dai nakeson yi”. Cikin kulawa da sabo da Garkuwa tace. “Kamar me kenan?”. Cikin yin ƙasa da murya tace. “Verging again inaso inje ayi min ɗinki tunda kinga Dr saurayi ne, kuma na haihu har yara uku, sannan yanzu shekara 7 kenan fa ba aure, to kuma ina tsoron ɗinki zafee”. Murmushin Garkuwar tayi tare da gyara zamanta kana tace. “Haba dai Ishmah kina tare dani kuma kike batun wani ɗinki ai wlh mun wuce wannan zamanin ke bar min wannan aikin a hannuna na rantse da Allah, zan baki mamaki in sha Allah zan maidaki tamkar ƴar shekara sha shida Batun kuma bazaki sha magani bata tasoba dolen dole nema Kisha magani, dan dole in gigita Dr Nafi'u in kankaro mana kimarki.” Sai kuma ta ɗan numfasa tare dacewa. “Amman batun ɗinkin da kikace, sai kiga Dr sun tabbatar mana cewa, babu ƙarin da kika samu yayin hayhuwa, *domin in dai ƙarine ma'ana yagewar wani sashin fatar HQ yayin hayhuwa ta sama ko ta ƙasa ko gefe more especially ma ace yagewar ta cikine, to zance na Allah dole sai dai ayi miki ɗinkin, domin babu wani maganin ko suplimet da zaija fatar data yage ta rabe da yar uwarta ace kawai a matsa magani ya haɗeta, wannan magana ce kawai ta mutanen mu masu saida magani dan son zuciya da son ciniki, fatar data ya yage kuma har yagun ya warke ace magani ya jawoshi ya haɗa, ni dai a karan kaina a yanzu Ban san wannan maganin ba in akwai wacce ta sani kuma ina biɗa*”. Cikin gamsuwa Ishmah ke gyaɗa kai tare da maida hankalinta baki ɗaya kan bayanan da Garkuwar ma'aratan keyi mata. Ita kuwa Garkuwa cikin faɗin gskyr abinda ta sani take da maganinshi tace. “Sai dai in buɗewace ta Normal hayhuwa, ko sakewa saboda yawan shekaru, ko kuma bazawar dake son sabunta budurci yayin aure, ko wanda iftila'in fyaɗe ya faɗawa, wanda ba yagewar, matsin ake buƙata to wannan bani da haufi akwai Maliƙi da Audugar babbar mace, sai kuma daɗi har maɗiga, su duka uku matsine, bani da haufi in dai matsine to magana ta ƙare, sai kin zama tamkar ƴar 15.” Cikin sauƙe numfashi Ishmah tace. “Alhamdulillah na huta da ɗinki kenan, dan last week na je naga Dr Fati, tace min bani da matsalar ƙari, wai ma fa cemin tayi kada in wani sha maganin matsi dan a tsuke nake”. Murmushi mai sauti Garkuwa tayi tare da cewa. “Eh fa kin san akwai mata masu jiki, roba ko hayhuwa sukayi a take suke komawa su tsuke su haɗe, kuma kullum a sabbi amare mazansu ke jinsu, to inko ke irinsu ce, nima bazan baki na matsinba”. Da sauri Ishmah tace. “A'a ba wanin nan ni ba irinsu bace, ke dai haɗani kawai ciki da waje”. “Uhhmmm fa Ishmah wlh ni ba ruwana ranar da zaki ji maza”. Murmushin tayi cike da kunya tace. “Haba kamar yarinya, ni dai a matseni, kuma a tsumani”. Kai ta jinjina tare da cewa . “To taso muje”. Ta ƙare maganar tana jan hannunta. Wani ɗaki na musamman suka shiga, wanda nanne store ɗin kayyakinta. Jujjuya idanu Ishmah ta farayi saboda ganin kayan ɗa'a kala da ban da ban, a cike maƙil ita kuwa Garkuwa. Fara sintar abubuwan da ya kamata tayi tana haɗasu wuri ɗaya. Cikin 30 minutes ta gama haɗa mata komai wanda ya kai na set ɗin 80k. Numfashi mai nauyi ta fesar tare da sasu cikin cart ɗin dake gefentakana ta turo suka fito tana cewa. “Kin dai gana shan maganin Infection set ɗin da na haɗa miki ko?” Suna shiga cikin Parlour tace. “Yes na gama shanye shi jiya shiyasa nace bari inzo yau ai”. Ta ƙare maganar suna zama bisa kujera 2 sitter. Botikin gumbar riɗi ta miƙa mata tare da robar gumbar ilanwaddihi sai gumbar madara, tana faɗin. “Su haka nake so ki rinƙa gutsura kina cinsu, ba tare da komai ba, duk da ba daɗi Amman dan Allah ki daure”. Sai kuma ta miƙa mata botikin gumbar da baya baiwa mai kishiya. “Shi wannan yana da masifar ƙarfi, kuma da ɗan gafi bazaki iya cinta hakaba, so ki rinƙa damawa da nono ko madarar ruwa kina sha. Sai kuma wannan garin mallaka ne ga kuma garin Belɗamhi. Su Kinga dai kamar kakarsu ɗaya green ɗaya ko”. Kai Ishmah ta gyaɗa. “Toh ba ɗaya bane, ga wannan farin kuma shine garin maɗi shima yana ɗan tsuke mace kaɗan duk da madara ko nono zakina shansu safe da yamma kullum. Sai kuma wannan Tsumin riɗi ne da kuma Tsumin makwaranyi da Tsumin goron tula shima yana matsi, su duk sha zakinayi, Ga kuma Tsumin tsirtai shi sai bayan biki zan gaya miji yadda zakiyi amfani dashi dan yana sa sha'awa”. Da sauri Ishmah tace. “Hmmm wlh kuwa kamar kin sani, ni bana jin sha'awa ko kaɗan wasu lokutan har ince ko dai bani da lfy ne, ko kaɗanfa bana jin sha'awa”. Tana miƙa mata ƴan ƙananan robobin Maliƙi daɗi har maɗiga, da Audugar babbar mace tace. “No lfyar ki ƙalau kwai kin cire batun namiji a ranki ne shiyasa, shekara 7 har na takwas ba namiji a rayuwarki, kin kuma tsare kanki shiyasa. Ga wannan kuma maliƙi ne da Audugar babbar mace. Su duk matsine shi Maliƙi da Audugar babbar mace suna da masifar matse mace, shi yasa ake haɗasu da daɗi har maɗiga domin shi kuma yana da masifar saukar da ni'imane. Yadda zaki amfani dasu. “Daɗi har maɗiga zaki fara matsewa, ki tabbatar yatsunki a bushe suke, zaki sashi can ciki. Sai ki ɗan lakati maliƙi kaɗan, sai ki saka Amman kar ya kai inda kika sa daɗi har maɗiga, sai ki rinƙa ɗan murza yatsarki kina ɗanyin ƙasa da ƴar diddigar haɗin maganin, ki tabbatar a take zakiyi haka dan wallahi kika barshi ya kai, 3 to 5 minutes yatsarki ma bazata shiga ba. Idan kina son matsewa over, sai ki ɗan yagi Audugar babbar mace kaɗan sai ki ɗan tura, ki barshi na awa ɗaya ki cireshi. Wlh idan kika barshi ya kwana yatsarki bazata shiga ta daɗi ba. Shi sai irin kamar saura kwana ɗaya bikin zaki fara yi shi a ƙalla kiyi kwana uku kinayi kaɗan-kaɗan, in kuma ma kina tsoro in kinyi sau ɗaya ya isa.” Ajiyan zuciya mai nauyi Ishmah ta sauƙe kana tace. “Hmmm sau ɗaya zanyi ma”. Ta ƙare maganar tana amsar rogar garin babambaɗe data miƙa mata da butar sirri. “Wannam butar tsarki zakinayi da ita, wannan kuma jan nama ko kaza zakiyi ta dafawa dashi a ƙalla kiyi sau uku. In sha Allah zan bada a fara Miki rubutun da zan dafa Miki zuciyar farin rago da kuma kazar rubutu da kuma turarukan wutanki dasu Humra da kulaccar sirri da dai sauransu, ni shine gudumowata”. Ruggume Garkuwa kawai tayi tare da fara zuba mata godiya. “Ni dai fatana inga kina aiki dasu”. Cikin jin daɗi tace. “In sha Allah kuwa, ngd matuƙa Aunty na ta kaina Allah ya ƙara rufin asiri”. Daga nan ta harhaɗa su a laida. “Wai wannan ledar fa ta meye”. Garkuwa ta tambaya tana nuna mata ledan data shigo dashi. “Huluna ne da takalma na seyowa Taj”. Jawo ledan tayi tana duba tsala-tsalan hulunan zannabukar da damanga masu masifar tsada sai kuma takalma duk kala bakwai-bakwai tana mai tsareta da ido tace. “Ishmah ke da Taj lamarinku na ƙona min ruwan kai fa, kin ƙi yarda cewa son juna kukeyi ko”. Da sauri tace. “Wallahi ba wannan mgnar a tsaka ninmu kunki ku yarda”. Ta ƙare maganar tana miƙewa tsaye. Itama Garkuwa miƙewa tayi tana faɗin. “Ko ɗazu kafin ki shigo naga wani Video da yayi da Hausa nayi ta mamaki wai yana cewa. “Assalamu alaikum mutanen Nigeria, ina muku fatan alkhairi ngd da chauraren karatuna da kukeyi, ina sonku sabodda Allah, ina gani nace Ishmah ce ta koya mishi”. Tana buɗe marfin motarta tace. “Wallahi kuwa nima ganin video kawai nayi, wani babban Malamine daga cikin malamanmu ya nemi yayi mgn da Hausa kana kuma suna gayyatarsa zuwa Nigeria buɗe wani babban masallacin a Borno da Abuja kin san ni da fulatanci muke magana amman dai zan fara koya mishi Hausar ma”. Ta ida mgnar ta shiga motar. “Ki gaida min Dadeyy da jiki”. Garkuwa tace lokacin da taja mota. Ethiopia Meymey ce zaune gaban iyayenta, cikin tsananin so da ƙauna mai tarin yawa Uncle Jibirin mahaifinta kenan yayi gyaran murya tare da cewa. “Allah yayi miki albarka Meymey na, Ubangijin talikai ya baki yaran da zasuyi Miki biyayya kamar yadda kikayi min”. Cikin jin daɗi da ƙara kifar da tunanin iyayen nata tace. “Amin ya Allah Daddy ni ka gama min komai da kayi min zaɓi da miji irin Yah Afif, miji mahaddacin Alkur'ani.” Cikin tsare fuskarta da ido Mommynta ta zuba mata ido dan san gano gsky ɗiyar tata, domin tafi kowa sanin makircin Meymey kuma sam bata gamsu da sauyinta ba, duk da dama bata taɓa fitowa ta nunawa mahaifin nata cewa bata son Taj ba, sai dai ita Mommy tana ganota. “Uhmmm Allah yasa da gaskene har ranki Meymey, domin iya gatan duniya dai mahaifinki yayi Miki da ya zaɓa miki Taj a matsayin miji”. Cikin kwaɓe fuska tace. “Mommy ai Yah Afif ya canci ko wacce mace ta soshi, Shi yasa nake alfaharin kasancewarsa mijina”. “Hhmmmm”. Shine kaɗai abinda Mommy tace. Dai-dai lokacin kuma Laylah ta dawo daga school, da sauri ta isa gaban Mommyn domin tana nuna mata so sosai, kana Meymey tun randa Taj ya tafi ta sauya sosai take jan Laylah a jiki, kasancewarta marainiya mai sanyin hankali da neman makusanta masu meye mata gurbin iyayenta da danginta data rasa yasa, tuni ta saki jiki da Meymey. Cikin kulawa haɗi da nuna bayyanenne so da jinƙai Meymey ta buɗewa Laylah hannun da sassarfa ta faɗa jikinta suka ruggume juna. “Baby Laylah kin dawo, gidan ba daɗi da kika tafi , Saida su Mommy suka zone naji ɗan daɗi gashi Yah Afif ma, tun ɗazu da ya tafi wurin Malam bai dawo ba”. Dai-dai lokacin Taj ɗin ya shigo bisa alamu tare suke da Laylah. “Daddy Barka da zuwa, Mommy yau kene da kanki”. Taj ya faɗa dai-dai lokacin da ya iso gaban Uncle Jibirin ɗin, cikin so da mutumtaka suka amsa, sai kuma ya juyo cike da mamaki jin Meymey na cewa. “Sweetheart kamar baka ganniba, saboda kaga Daddy da Mommy ko”. Ƙanƙantar da idanunsa yayi tare da cusasu cikin nata idanun yana nazartan sauyinta da ya samu tunda ya dawo. “Hmmmmm”. Yace a ransa a fili kuwa cewa yayi. “Neman tabarraki nake, kin san Allah da girma iyaye da girma, ka bisu ka dace ka saɓa musu ka taɓe”. Ya bata mgnar da kurman baƙi da ita yake. Sai kuma tayi murmushi tare cewa. “To bari dai in kawo maka ruwa”. Jim kaɗan ta dawo da goran ruwa mai sanyi tare da cup amsa cup ɗin yayi. Yana kallon Laylah dake maƙale da Mommy tana cewa. “Mommy mun kusa zuwa Nigeria nida Uncle Taj, zanje Afirka inga Black peoples, kinsan ana cewa Black is beauti wai sun fimu kyau ko?”. Da sauri Uncle Jibirin yace. “Sosai ma kuwa”. Nan dai suka ɗanyi hira kana su Uncle Jibirin suka sallamesu suka tafi suna sa musu al'barka. Washe gari Ishmah ce ke draving a hankali saboda Dadeey tace yau so take taga Hajiyarts mahaifiyarta kenan. Shiyasa Ishmah ta ɗauki Dadeey dan ta kaita wurin mahaifiyarta su kuma kakarsu. A hankali taƙe ɗan motsa lips inta tana cin gumbar riɗin da robar ke gefe, lunshe idanunta tayi tana jin garɗin riɗin na mata daɗi, jin alamun saƙo ya shigo wayarta ne yasata ɗan duba a fili tace. “Kai Dadeey kallifa kuɗin da Taj ya turo min har dubu ɗari takwas.” Cike da mamaki Dadeeynta tace. “Ikon Allah to na menene haka kuma”. Tana danna mishi kira tace. “Bari in tambayeshi”. Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga dai-dai lokacin da yake fitowa daga side ɗinsa ya nufi babban Parlour da dole ta nan zai fita. “Taj wannan kuɗinfa na menene?”. Cikin sanyinsa yace. “Ki saya waya, ne dan nasan wayarki zata samu matsala”. Da sauri tace. “Saboda me”. Cikin tunano mafi akasarin lukata abubuwa kan farun musu a tare kamar yadda mafi akasarin abubuwan su iri ɗaya ne. “Saboda wayata ta faɗi ɗazu ta fashe, ko kin manta komai namu a tare yake zuwa”. Cikin dariya tace. “To meyasa kayi aure ni banyi ba?”. Ido ya lumshe tare da cewa. “Eh Amman kuma ai inada matsaloli akan aurarrakin da kuka cusamin kamar yadda kike da matsala kan aure”. Cikin sanyi tace. “Yanzu ina driving in mun isa zan kiraka Dadeey ta gaidaka”. “Ina amsawa, ina zakije baki nemi izinina ba”. “Afwan Dadeey zan kai wurin Hajja Ummanta”. Dai-dai lokacin da ya iso Parlour yace. “Toh sai anjima”. Daga nan suka katse kiran. Suna isa Ishmah nayin parking tayi saurin fitowa dan buɗewa Dadeey ƙofa, da sauri ta riƙe kanta saboda jin tasss wayarta dake kan cinyarta ta faɗi kan intalok ɗin, idanutan ta zubawa wayar ganin yadda screen ɗinta ya fashe yayi ratsa-ratsa. Taj kuwa cikin mamaki yake kallon Meymey dake zaune bisa kujerar 3 sitter, Laylah na kwance kan kujerar tayi pillow da cinyar Meymey, ita kuwa Meymey tana... Hmmmm wasanfa na musamman ne ni kaina tsumani yakeyi! By *GARKUWAR MARUBUTA* ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** [1/8, 5:26 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 8* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin INDA RAI na kiɗine 1k ne kacal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097583276. Mutanen kasar Niger kuma 1000fc ne jaka ɗaya kenan +22790899076 ga number Mommy ita zakuyiwa mgn* Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma sdw, da dai sauran abubudann ban lissafa Sune manyan alamomin infection. Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi. Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa. KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa. INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki. Idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA. Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh ai duk nisan state da kike ba ruwan mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in kinsan Baki shirya sayan kaya ba kuyi haƙuri kada kumin mgnar ku bari sai kun shirya,kada kuzo mu ɓatawa juna lokaci Allah y sni na tsani harkar ƙranta🙈🤗🤣, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi duka.... Tana tubke mata gashin kanta tare da kitsen mata jelar, suna hira da dariya, domin sosai Laylah ta sake da ita. Ita kuwa Meymey jin motsinshi ne da ƙamshin turatensa yasa ta juyo ta inda yake tare da mishi wani irin kallon da yasa kanshi kullewa yana mai nazartan abinda kallon ke nufi. Sai kuma ya maida dubansa kan Laylah dake cewa. “Uncle Taj gobe al'hamis ba school ba hadda zanje gidan Ummeey”. Sai kuma yayi shiru jin Meymey na cewa. “Laylah ki tafi ki bar Aunty Meymeynki ita ɗaya”. Murmushin tayi tare da cewa. “Ga Uncle Taj.” Bata kulata ba sai cewa tayi. “Kiyi haƙuri Laulah sai jibi Friday zamuje mu wuni can”. Cikin gamsuwa tace. “Toh Allah ya kaimu”. Amin tace. Shi kuwa Taj ko ƙala bai ce musuba, ya fice daga falon. TAJMUH CONSOLATION HOSPITAL ya wuce. Shine bai tasoba sai ƙarfe tara na dare saboda patients sunyi yawa. Cike da gajiya ya zare rigar jikinsa. Ya rage daga shi sai boxes. Bathroom ya shiga. Bayan kamar 40 minute ya fito cikin wani towel ɗin baccisa Cotton sai baza ƙamshi yake dan shi baya iya takure kanshi in zai kwanta. Bakin gadon sa yana mai haɗe tafukan hannunsa ya fara addu'an bacci. Bayan ya gama ne, har zai konta kuma sai yaga wayarsa na haske cikin bacci da gajiya ya amsa kiran. “Kamin baki ya kuma kamani”. Ishmah ta faɗa cikin narkekkiyar murya. “Wayarki ta samu matsala ko?”. Ya tambaya yana ɗan buɗe idanunsa. “Eh muna isafa na fito cikin mota na mance wayata na kan cinya tayi ruyu-ruyu”. Murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Komai namu iri ɗaya”. Numfashi mai cike da alamun mamakin yadda abubuwa su ke kasancewa a tare tayi kana tace. “Amman dai nayi sa'a bata ɗaukeba, an min ɗauke min ɗin duk abubuwan daga tsohuwar zuwa sabuwar, Dadeey tace a gode maka”. “Wacce collor kika saya”. “Iphone 14 pro max ce, white collar ”. Cikin Muryar bacci yace. “Shima iri ɗaya, da har zan sayi Samsung Galaxy sai kuma na tuna itace ta fashe nace bari in canza, kuma nima ina fita a mota ne ta fashe”. Tana shafawa Dadeey magani tace. “Toh Allah dai ya tsaida kamanceceniyar munnan kan alkhairi”. Amin yace, daga nan sukayi ɗan hira kana sukayi Saida safe. Washegari ranar Alhamis, da yamma, Ishmah ce zaune gaban Dadeey tana yanke mata farce, Rahama da ta dawo saboda hutun da suka samu na school tana ɗan matsa mata ƙafar, suna waya da Khadijah cewa Gobe zatazo daga Gombe zuwa Yola duba jikin Dadeey. Abban su kuma yana bayan Dadeey yana hira da yaran nashi. Aunty Nana matar Yah Muhammad da Aunty Maryam, ne suka shigo da womers a hannunsu, kamar kullum kasancewar a gidan suke kowa da part ɗin sa mai girma da gate a tsakaninsu ma sai dai bayan BQ part ɗin su Dadeey ne forko. Wanda gefen Abba two bedrooms ne da babban Parlour sai Dinnin area, kana fita side ɗin abban kuma sai wani ciki da falo wanda nanne ɗakin Adam da Hamisu, sai side ɗin Dadeey itama 2 bedroom ne sai ɗan ƙaramin ɗakin da masu aiki suke zama a da can baya. Sai kitchen da store wanda Ishmah ke ɗan musu abun ƙwalama. Gefen Yah Muhammad da Yah Abubakar duk part ɗinsu kamar na Dadeey ne. Kasancewar suna gida ɗaya yasa su Dadeyy basa girki, womers ɗin Abba da ban sai kuma na Dadeyy sai kuma suke sawa a babba na Ishmah da Adam da Hamisu. Cikin son surkan Dadeey tace. “Sannunku ƴan al'barka, Allah ya ƙara lfyar aiki”. Amin suka amsa a tare. Sai kuma suka haɗa baki wurin cewa. “Dadeey ya jiki?”. “Da sauki sosai ma”. “Toh Allah ya ƙara sauƙi”. Amin Ya Allah sukace baki ɗaya, sai kuma suka gaida Abba. Da sauri duk suka kalli Ishmah jin yadda ta saki wani irin ƙara tare da yarfa hannunta. “Ayyah sannu Boɗɗina kin yanke ko?”. Cewar Dadeey. Ishmah ba dai rakiba tuni ido ya ciko da hawaye. Abba kuwa hannunta ya kamo yana cewa. “Sannu Mamana zo inyi miki tofi”. Ya ƙare maganar da farayi mata tofi, wanda bisa haka suka raineta Saboda yawan rakinta da saurin kuka yasa komai sai Abba yace zo in Miki tofi da ya fara mata tofin kuwa zataji sauƙi. Murmushin Aunty Nana tayi tare da cewa. “Saboda ɗan wannan yankanne kike wannan raki, da yarfa hannun”. Aunty Maryam ce ta amshi zancen da cewa. “Bakiga duk tabi ta ɓata mana yara da raki da saurin kukaba, ga shegen tsoro, hakafa Khairat jiya daga ɗan faɗuwa in kinji ihun da take zubawa ke kyace ido ake cire mata”. Murmushi Dadeey tayi dan tasan mgnar su gsky ne. Su kuwa cikin wasa irin na matan wa da ƙannen miji sukaci gaba da mata tsiya. “Uhmmm ai dan ciwon ba a jikinku yakeba, shiyasa kuke cewa raki, ke kam ma Aunty Nana kin manta randa kunama ya harbeki kika hanamu bacci a asibitinmu”. Dariya Rahman tayi Aunty Nana kuwa da sauri tace. “Toh ni nama tafi”. “Yoh da ki tsaya mana”. Cewar Rahman, itama Aunty Maryam dari tayi tabi bayan Nana. Bayan sallan Isha Zailanee ne, zaune a tsakiyar Parlour ya baza ɗinkunan da ya fesawa Taj. “Kai Masha Allah, gsky Zailanee kayi ƙoƙarin”. Yah Muhammad dake cin abinci da Ishmah da Rahama a plate ɗaya ya fadi, domin ba ƙarya ya watsa musu ɗinki na gani na faɗa, hulunan da takalman da Ishmah ta saya ya rinƙa haɗa ko wanne da kayan da zai tafi dashi yana ninkewa. Ita kuwa Ishmah janye hannunta tayi daga cin abincin ta jawo mug ɗin da ta dama gumbar da bawa mai kishiya da kuma garin Belɗamhi da garin mallaka, ta ɗan fara sha da spoon ɗin tare da cewa. “Uhmmm Allah dai yasa suyi mishi dai-dai”. Da sauri yace. “In sha Allah sunyima sun gama, ga na Abba da Mahmud da Khalid ma da kika kawo daga baya na ɗinka”. Jin Muryar Idris telan ne yasa tace. “Yauwa dama yanzu nake tunaka a raina”. Shigowa yayi tare da ajiye ƙatuwar ledan kayanta dana Dadeey sai na ƙannenta Khadijah Hafsat Rahama sai ɗiyarta Mitan. Ganin ta meda hankali kansa ne yasa Zailanee sallamansu ya tafi. Nan shima Idris ya rinƙa fito da ɗinkunan nasu ɗaya bayan ɗaya. Na Dadeey ta haɗa guda biyar tare da cewa Dadeey ga naki”. Amsa tayi cikin jin daɗi tace. “Toh Boɗdina ngd Allah yayi Miki albarka ya nuna min aurenki. Allah yasa rai akayiwa”. Amin sukace baki ɗaya. Ita kam Ishmah sai murmushi take saboda masifar kyau da ɗinkunan sukayi. “Idris naga na Dadeey duka biyar ya dawo haka nasu Rahama duka uku-uku sun dawo ni kuma nawa kamar dai 20 na bada kuma sai naga 16 ina huɗun?”. Yana ɗan sosai ƙeya yace. “Ban haɗusuba shiyasa na dawo da waɗannane dan sun cika min shago”. Cikin gamsuwa tace. “Toh ba matsala, bari in turama sauran kuɗinka kai da Zailanee”. Daga nan ta tura mishi kana ya sallamesu ya tafi. Yau Jumma'a kamar kullum gidan Malam cike yake da yaransa kasancewar wannan karon makarantu da dama sun tafi hutune yasa gidan yafi ko yaushe cika saboda taron jumma'an yau ɗin harda jikoki da surkai baki ɗaya. Meymey ce zaune da Ummeey sunata hira, Wanda hatta su Maryam sunyi mamakin sauyinta, domin da batama cika zuwaba, gashi yau harda abinci tayi kala-kala ta kawo. Koda aka dawo sallan azahar gaba ɗaya ƴaƴanshi da jikokinsa suna cike a Parlour cikin jin daɗi ya kalli durkanshi dake genfeshi tare da ajiye womers ɗin abincin da suka kakkawo, cikin so da jin daɗi yace. “Yau duk kuyi haƙuri abincin gidan Abbana zanci”. Kusan duk murmushi da yawan cikinsu sukayi wasu muka sai cewa sukayi. “Malam munyi haƙuri amman asamana al'barka”. Irinsu Aryan kuwa zuciya ta ƙuntata, hakama Mom Amal. Ita kuwa Meymey cike da jin daɗi tace. “Malam ngd”. Shi kuwa Taj dake tsakanin Malam da Yan Yusuf ƙasa yayi da kansa yana nazari kan sauyin Meymey da zuwa yanzu ya fara tsinkewa da lamari. Haka dai ranar ma aka wuni. Misalin ƙarfe 9:00 pm Taj ɗinne zaune gaban iyayen nashi cikin girmamawa yace. “Malam na tura kuɗin asibitin nan na Qatar, ashe harda gidajen ma'aikata ma a cikin asibitin duk sai ɗazu aka ƙara turo min video komai, sunyi ginin bisa tsari mai kyau sosai, duk kayan aikin da sukayi amfani dashi mai kyau, kuma hatta ababen aikin na asibitin sun zuba komai, saboda su haka sukeyi a ƙasar yanzu maikata kawai zan nema, dai kuma na'urorin da zan buƙaci ƙari, toh gashi dama inada masu neman aiki sosai damu a TAJMUH, zan nemu wasu daga ciki in turasu can. Dan harda gidajen ma'akatama akwai, bayan nawa da ke nagefen cikin asbitin”. Cikin gamsuwa Malam yace. “Masha Allah ai haka dai Hafiz yace min daya dawo”. Da sauri yace. “Malam ka turashi yaje ya ganine?”. Kai ya jinjina mishi tare da cewa. “Eh duk da kace min kaje ka gani ban gamsuba Saida na tura Hafiz dan kai na sanka da sanyin hali da rashin bincike. Gashi kuma sai kwanan kasan harda gidaje a ciki. Hafiz kuwa hatta Restaurant masallaci dake ciki Saida ya ɗaukomin Saida na gani kafin nace ka biya. Allah ya sanya alkhairi yasa rai da lfy su mara yasa a fara aiki a ciki a sa'a”. Cikin jin daɗi kulawar iyaye kan yaransu duk girmansu yace. “Amin Amin Ameeeeeeeen Ya rabbil izzati ngd matuƙa Yah Abana Allah ya ƙara girma”. Amin sukace tare da sa mishi al'barka kana ya sallamesu ya tafi. Yau saura kwana uku tafiyan Taj da Laylah zuwa Nigeria. Zaune yake gaban Ummeeyshi yayinda Malam kuma ke gefe a kishinƙiɗe gyara zamansa yayi tare da cewa. “Yah Abana. Ummeey tafiyrmu fa saura kwana uku”. Murmushin tayi tare da cewa. “Yanzu wato dai Laylah ta dage sai kunje tare ko”. Sai kuma Suka kalli Malam ɗin da ya tashi zaune tare da cewa. “Nigeria! Nigeria!! Nigeria!!! Abbana Nigeria zakaje, Nigeria!!!”. Yayi ta maimaita sunan ƙasan ransa tare da kira sunan da wani lafazin dake fitowa daga can cikin rai da jini da zuciya. Sai kuma ya koma ya kishingiɗa tare da cewa. “Nigeria”. Cikin sanyi Taj yace. “Yah Abana ko akwai matsala ne”. Cikin jujjuya kai yace. “Ba matsalar komai Tajuddeen kaje Allah ya kaika lfy ya dawo da kai lfy”. Cikin mamaki yace. “Amin ya Allah”. Dai-dai lokacin kuma Dr Nafi'u ne ke waya da Ishmah. “Yau saura kwana nawa ne kam”. Cewar Ishmah. “Saura kwnan goma cib”. Murmushin jin dadi yare da cewa. “Kwanakin ma kamar basa gudu”. Da sauri tace. “Afwan bari in zo”. Ta ƙare maganar tare da fitowa Parlour saboda jin Muryar yan kyawawan yaranta, Mahmood ɗan 13 yaers Minat 10 yaers Khalid auta 8 yaers. Cikin zuba musu ido tana kallon kyan haibarsu ta buɗa musu hannun ta, kusan a tare suka ruggumeta. Daga nan suka zube a tsakiyar Parlour. Jiyo hayaniyarsuce tasa Dadeey da Rahma dake Bedroom ɗinta fitowa. Da sauri suka nufi Dadeey suna. “Oyoyo Dadeey ya jikinki, Babanmu yace mu gaidaki da jiki”. Ta shafa kansu tace. “To ai zaku kadani, baku san ƙafar Dadeey ba ƙarfiba, ngd Baban naku yana lfy ko”. Alhamdulillah sukace kana duk suka koma gaban Mahaifiyarsun. Khalil ta jawo jinkinta tare da cewa. “Autana zo mana inji me kakeci haka na ganka Masha Allah”. Murmushi yayi tare da kife kanshi a jinkinta, Minat kuma ɗan baki ta tura tare da cewa. “Mimi kamar fa kin fiso Khalid.” D sauri ta jawosu duka ta ruggume tana cewa. “Duk ina sonku Allah ya raya min ku yayi muku al'barka”. Amin Amin sukace a tare. Bayan kwana biyu. Ethiopia Zaune yake a office nashi, yana riƙe da waya, bini-bini ya kai wayar kunne. Ido Dr Abbas ya zuba mishi cike da mamakin yadda gaba ɗaya hankalinsa ke kan wayarsa. “ What's going on?”. Dr Abbas yayi tambayar cike da tson fahimtar menene matsalar sa. Ɗan gajeren tsaki yaja tare da lumshe idanunsa da suka fara sauya lani muryar can ƙasan maƙoshinsa yace. “Ishmah”. Kai Dr Abbas ya jinjina tare da gyara zaman yace. “Uhmmm ai dama na sani a rina, To meke faruwa”. Yana mai buɗe idanunsa yace. “Yau 2 days kenan bamuyi wayaba, jiya da shekaran jiya duk bamuyi wayaba, yauma tunda safe kiranta nake Amman yau wayar ma bata shiga, shekaran jiyan har Yah Muhammad ɗinta na kira shima bai ɗaukaba, na kira Abba shima baiyi piking call ɗin naba. Hankalina ya tashi, gashi dama gobe zan wuce Nigeria to, kuma sai suka sauya lokacin tashi, wai sai jibi. Duk rintsi Ishmah kan nemeni muyi mgn nayi mata miss calls sama da 23 a kwana biyun nan”. Sai kuma yasa hannunsa duka biyu ya riƙe kansa tare da fesar da numfashi mai nauyi. “In sha Allah ba komai, ka nitsu zuwa jibi kafin ku tashi zaka samu wani daga cikin mutanen ta ko ita kantama”. Yana miƙewa tsaye tare da ɗaukar briefcase ɗin shi ya fice yana cewa. “Allah yasa haka”. Shi kuwa Dr Abbas bayan shi ya biyo yana faɗin. “In ance son juna na gab da fasa muku zuƙata ya kasheku sai ku ƙi yarda, yanzu gani duk yadda ka shiga ɗimuwa, dan kawai kunyi kwana biyu bakuyi wayaba”. Ko ƙala bai ce mishiba, har Saida suka sauƙa ƙasa kana yace. “Kazo ka sauƙeni a gida, dan Abu Hashim baya kusa. To yace tare da lolubo key ɗin motarsa. Washe gari, yau kwana uku kenan bayyi waya da Ishmah ba, kana gobe da asuba jirginsu zai tashi daga Ethiopia zuwa Abujan Nigeria. kwance yake a tsakiyar Parlour Addawa yayi ringine idanunsa a rufe duk da bawai bacci yakeba. Ita kuwa Addawa zaune take a gefensa ta zuba masa ido, tamkar wacce ke kallon TV, kallon nashi takeyi kuma cike da nazari, tausayi, da kuma fargabar kada damuwa tayi mishi illa a wani sashi na zuciyarta kuwa addu'a take, kada Allah ya tabbatar da wasu daga cikin mafarkanta a kanshi. Numfashi mai nauyi ta fesar cike da so, kulawa, ƙaunar jikin nata, mafi soyuwa a gareta tace. “Taju! Taju!!! Taj....”. Ta ƙarashe kiran sunansa da sunanda da tasan shi Ishmah ke kiransa. Cikin yanayi mai cike da rauni, damuwa, fargabar rashin sanin halin da Ishmah ke ciki ya buɗe idanunsu da rashin bacci da damuwa ya sauya launinsu, zuba mata idon yayi ba tare da yace ƙalaba, ƙara matsoshi tayi tare da cewa. “Ba dai kace in sha Allah gobe da asuba jirginku zai tashi zuwa Nigeria ba?”. Kanshi ya gyaɗa mata yana mai rufe idanunsa. “Toh ka tashi kaci abinci, in sha Allah gobe uwar haka dai kana tare da Ishmah”. Murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Addawa 3 to 4 Days fa kenan banji Ishmah ba, batayi min text ba, batayi min mgna ta Whatsapp ɗin da tasan domin ta ne, kawai na buɗeshi nake kumayin mgn da ita kaɗai, ban san wani hali Ishmah ke cikiba, ban san me yake faruwa da itaba”. Ya ƙare maganar yana kife kansa bisa ɗan pillow kujerun. Ita kuwa Addawa kasake tayi tana ƙara jinjinawa lamarin, domin a iya tsawon rayuwarta Taj bai taɓa jeranta mata doguwar mgna haka ba yankewa ko jan numfashi ba sai akan Ishmah, ta dai san mutum ɗaya kam suna doguwar mgnar datafi hakama tsawo shine marigayi kakansa, wanda kuma mgnar tasu kan ta'allaƙa ne kan karatun ƙur'ani da yake bashi hadda. Da sauri ta ɗago kanta jin Muryar ɗiyartata da kuma surkinta. Cikin sauƙe numfashi tace. “Alhamdulillah kunzo a dai-dai”. Sai kuma ta kalli Taj ɗin da zubawa iyayen nasa idanu cike da tarin damuwar dake ɓoye can ƙasan zuciyarsa da idanunsa. “Bismillah ku iso ku zauna” Cewar Addawa. Bisa kujerar 3 sitter dake bayan Taj ɗin suka zauna. “Abana matso nan kusa dani”. Malam ya faɗa cikin kulawa. Ummeey kuwa hannun tasa ta kamo hannunsa wanda hakan ya sashi masowa kusa dasu, a tsakiyarsu ya zauna a ƙasa, kusan a tare suka ɗaura hannunsu a kanshi tare da haɗa bakin wurin cewa. “Meke damunka, Afif ka gaya min”. Ummeeyshi ta ƙarashe mgnar. Sai kuma ya ɗago kansa ya kallesu kasancewar suna fuskantar juna. A hankali ya kalli warshi dake gefenshi, cikin tsananin sauri yasa hannunsa ya jawo wayar tare da yin piking call ɗin sabida ganin sunan Yah Muhammad. Murya a sarƙafe yace. “Assalamu alaikum, Yah Muhammad, meke faruwa? Ina Ishmah? Ya jikin Dadeey?”. Ya jero mushi tambayoyin a lokacin guda ba tare da ya bari ko sallamarsa ya amsaba. Cikin sanyi murya mai cike da rauni Yah Muhammad yace. “Wa alaikissalam Taj, Dadeey'mu ta warke cuta ya gagara, ya ɗauke mana ita tun kwana uku baya, Ishmah'nka ta zama tamkar kurma bata mgna sai binmu da idanu, bata bacci.” Tunda ya fara mgnar jikin Taj ya ɗebi wani irin rawa da tsuma tamkar wanda aka jonawa choking. Cikin ƙarfin imani da tawakkali ya samu ya fizgo kalmar. “Innalillahi wa innalillahi rajiun”. Sai kawai yayi ta maimaita kalmar tamkar wanda ya fara rasa nitsuwarsa, sai wani sarƙafewa da karkarwa muryarsa keyi. Da sauri ya rumtse idanunsa tare da kifa kanshi kam cinyar Ummeynshi yayinda hamnunsa ɗaya kuma bisa cinyar Yah Abana. Yana jin duk abubuwan da Yah Muhammad ke cewa Amman ya gaza iya control ɗin harshensa bare ya samu ya iya faɗin wani abu. Haka yasa Yah Muhammad ya dawo yana bashi haƙuri sabida fahimtar ya ɗimauce labarin rasuwar Dadeey ya daki ƙahon zuciyarsa. “Kayi haƙuri Taj, Dadeey addu'armu take buƙata duk yadda muke sonta Allah da ya halittata mana ita, ya bamu ita a matsayin mahaifiya ya fimu sonta, ni na kiraka da ƴa ƙinin kaine zaka iya kwantarwa da ƙanwata hankali ka taushi zuciyar Ishmah”. Sai a lokacin ya iya cewa. “Ummeey Ishmah. Ummeey Ishmah Dadeeynta ta rasu, ita kuma bata mgna bata bacci. Ummeey Ishmah! Ishmah!! Ishmah!!!”. Sai kuma ya kama lip inshi na ƙasa da haƙoransa ya ciza da ƙarfi. Cikin kulawa da tausayin Ishmah Ummeey da Addawa da Yah Abana suka haɗe baki wurin faɗin. “Innalillahi wa innalillahi rajiun. Allah sarki rayuwa, Allah ya Ubangijin talikai ya jiƙanta da rahama yasa ta huta”. Yah Muhammad kuwa katse kiran yayi, fahimtar Taj ɗin yana tare da iyayensa. Shi kuwa Taj sunan Ishmah kawai yaketa maimaitawa. “Kayi haƙuri Taj Ishmah zata samu lfy, rashin mahaifiyarta ne ya daki zuciyarta, in ka isa ka taushi zuciyarta ka ƙarfafa mata guiwa ka girgiza imaninta ka hibɓasa mata, aminta da yarda da ƙaddararta.” Yana mai rumtse idanunsa yace. “Yah Abana wai bata mgna bata bacci fa.” Kanshi Ummeeyshi tare da cewa. “In sha Allah komai zai dai-dai ta”. Addawa kuwa kai ta sunkuyar hawaye na tsiyaya tausayin Ishmah na ratsata, duk wanda ya rasa uwa shi ne kaɗai yake iya sanin ciwon da zuciyar wanda ya rasa nasa. Ganin haka ne kuma yasa Ummeeyshi komawa gefen mahafiyar tata tana bata baki, nan dai sukayi ta tausarta. Washe gari, jirginsu na sauƙa a Abuja. A kuma dai-dai lokacin passingers ɗin jirgin da zai tashi daga Abuja zuwa Yola suke ta shigowa Airport ɗin saboda saura awa ɗaya jirginsu ya tashi. Saukarsun ba jimawa, suka shiga jirgin da zai kaisu Adamawa Yola ƙarfe ɗaya dai-dai suka dira cikin Yola international Airport. A hankali suke sauƙowa daga saman steps ɗin da yafi kama da na dakekken kwano. Hannunsa riƙe da hannun Laylah daketa baza idanu tana kallon yanki ƙasar da bata taɓa zuwaba. Shi kuwa Taj a hankali yake take steps ɗin tare da lumshe udanunsa, yana mai tariyo da nazarto duk kwatancen gidansu Ishmah, hatta gidajen yan uwanta da sunayen anguwaninsu kab zai iya kai kansa kamar yadda itama zata iya kai kanta gidansu Taj dama duk yayunshi maza. Yar gajeriyar tafiya sukayi kana suka shigo cikin muhallin da za'a kawo musu kayansu. Shigarsu ba jimawa, na'urar ta fara juyawa, cikin sa'a a sahun farko jakarsu ce a gaba, hannunshi ya kai da niyar ɗauka sai kuma yayi saurin jenye hannunsa saboda ganin wani ɗan matashi yasa hannunsa ya ɗauke masa jakar tare da sakin yalwataccen Murmushin kana yace. “Alhamdulillah yau Sheykh Afif Muhammad Taj ne a ƙasata Nigeria kuma jihata mahaifata. Faɗin hakane da yayi ya jawo hankalin mafi kusa dasu, nan da nan mutane suka zagayeshi, cikin ɗan sakin fuska yake basu hannunsa suna musabaha. A haka dai har suka fito farfarjiyar da masu tarban mutane ke tsaye. Da sauri Yah Abubakar ya nufi inda Sheykh Afif ɗin yake. Yana isa ya ratsa tsakanin mutanen dake zagaye dashi, tare da miƙa mishi hannun. “Suna Abubakar Abdullahi Matawalle... Sai kuma yayi shiru jin Taj ɗin na cewa. “Yah Sadiq”. Murmushin Yah Sadik yayi fahimtar Taj ɗin yayi masa farin sani a hoto, ruggume juna sukayi, sai kuma ya kalli Mahmud ɗan Ishmah tare da miƙa mushi jakar Taj daya amsa a hannun ƴaron nan. Da sauri ya riƙo hannun Taj kana juya ya nufi motarsu tare da cewa Bismillah. Shi kuwa Taj hannun Laylah ya kuma riƙewa, tare da bin bayansa. Suna isa bakin motar wasu jama'ar suka kuma zagayeshi tare da fara bashi hannun suna kuma matsoshi dayin selfee. Cikin mutumtaka Yah Sadik ya ɗan kallesu tare da cewa. “Kuyi haƙuri ku bashi hanya, yana tare da gajiya yanzu ya sauƙo daga Ethiopia ko ruwa bai shaba”. Yayi mgnar cikin fillancin, jin haka ne yasa suka bashi hanya, tare da buɗa mishi marfin dalleliyar motar Yah Sadik ɗin, yana shiga Laylah ta shiga sai kuma ya jawo hannun Mahmud tare da cewa. “Shigo nan”. Cike da nitsuwa yaron ya shiga bayan ya zauna kusa dashi. Shi kuwa Yah Sadik motar yaja tare da cewa. “Barka da zuwa Sheykh Afif”. Yana ɗan kallon Mahmud yace. “Barka dai Yah Sadik, ya ƙarin haƙurinmu?”. Cikin sanyi Yan Sadik yace. “Alhamdulillah”. Kai ya ɗan juya da kyau yana kallon Mahmud tare da cewa. “Allha ya jiƙanta da rahama yasa ta huta, mu kuma Allah ya bamu haƙuri da juriyar rashinta”. Cikin ɗan rage gudun motar Yah Sadik yace. “Amin Amin Ameeeeeeeen Ya rabbil izzati”. Dai-dai lokacin kuma suka fito Airport ɗin. Shi kuwa Taj a hankali ya ɗan riƙo hannun Mahmud tare da cewa. “Yah Miminku tana mgna?”. Fuska a raunace ya girgiza kai tare da cewa. “Bata mgna har yanzu, bata sanma kazo ba!”. Ya ƙare maganar idanunsa na ciccikowa da hawaye. Kanshi ya shafa tare da jawoshi jikinsa cike da son yaron yace. “Zo nan my Son karkayi kuka, in sha Allah zatayi mgn”. Sai kuma ya kalli Laylah da batajin fillancin ko kaɗan sai larabci, turanci, da kuma yarensu na Palastine da Omoro data fara koya wurin su Addawa da Zulaihat . Saboda bata wani daɗe a Ethiopia ba bare taji fillancinsu da shima ya ɗan bambanta kaɗan da namu, iya gaisuwa kawai ta iya. Sai dai jin Mahmud nayi larabci ne yasata sakin jiki ta fara mishi mgna. “Ina Anty Ishmah?”. Yana kallonta yace. “Mimina?”. Sai kuma ta kalli Taj, kai ya gyaɗa mata alamar eh Ishmah ce Miminsa, ganin haka ne yasa tace. “Eh ita”. Dai-dai lokacin kuma suka iso kwanan masallacin juma'a na Anguwarsu wanda nanne kwanan gidansu Ishmah tsakaninsu da Airport koda ƙafa zakaje. Suna isa bakin masallacin ana kiran salla azahar. Gefen masallacin jumma'a kaɗan ya ɗan rasa ya wuce gaba kaɗan. Tare da fuskantar Gate ɗin gidan nasu tare da yin Hon. Da sauri maigadin nasu ya buɗe gate ɗin. Wani sassayan numfashi mai tsawo Taj ya fesar tare da lunshe idanunsa saboda sassayan iskan gidan dayake cike da shuke-shuke musamman banana da yake ta ko ina, sai kuma flowers dake zagaye da gidan da hakanne yasa gidan yin sanyi mai daɗi a jikin ɗan adam. Yah Sadik nayin parking Laylah da Mahmud suka fita a tare, sai kuma Yah Sadik ɗin da Taj suka fito a tare dai-dai lokacin kuma Abba, Yah Muhammad Adam, Hamisu, Barrister Kamal, da Mukhtar Bappa Kawai suka fito daka cikin gidan bisa alamu sunyi al'wale dan tafiya salla. “Masha Allah, Tajuddeen ka iso, sannu da zuwa Nigeria”. Cewar Abba, sai kuma Yah Muhammad dasu Adam sukayi saurin nufosu suna faɗin. “Barka da zuwa Yah Taj”. Shi kuwa Taj da sauri ya nufi Abba tare da ɗan rage tsawonsa kaɗan yana miƙawa Abba hannu sai kuma ya miƙe tsawon nasa ganin Abban ya buɗa masa hannun alamun yazo. Ruggume juna sukayi cike da mutuntaka. “Bismillah Sadik kaishi Parlour na, ka kira Auta ta kawo mishi abinci”. Sai kuma Yah ƙare maganar yana kallon Laylah dake riƙo hannun Taj ɗin tana faɗin. “Uncle Taj ina Aunty Ishmah”. Kan Laylah Abba ya shafa tare da cewa. “Mahamuda kaita wurin Khadijah zata kaita wurin Mameenku!, Sai kazo mu tafi masallaci”. Sai kuma yayi murmushi jin Taj na maida mata abinda ya faɗa da larabci Ai da sauri tabi bayan Mahmud suka nufi cikin gida, dai-dai lokacin kuma Khadijah ta fito daga Parlour Dadeey zata nufi part ɗin Yah Muhammad. Da sauri ta kalli Mahmud dake gaya mata sakon Abba. Cikin sanyi ta ɗan sunkuyo tare da kama hannun Laylah tare da sakar mata ɗan sassayan murmushi tace. “Toh zo muje muyi salla, itama Aunty Ishmah tana salla ne”. Ta ƙare maganar cikin tattaro ɗuk iyakar luggar larabcin bakinta. Mahmud na juyawa yace. “Tana jin turanci ai ba iya larabci ba”. Cikin dauƙe numfashi Khadijah tace. “Ato da sauƙi”. Daga nan taja hannunta suka tafi. A can harabar gidan kuwa, cikin son juya fillancin Ethiopia zuwa na Adamawa Taj yace. “Muyi salla tukuna Abba”. Kai Abba ya gwaɗa tare da cewa. “Toh kuyi al'wala”. Yana kallon Yah Muhammad dake cewa. “Eh muje kayi al'wala”. “Inada alwala”. Jin haka ne yasa duk suka wuce masallacin. Suna shiga ana ƙoƙarin tada iƙama, ganin shine yasa Limamin yin saurin juyowa ya fuskancesu da kyau cike da son tabbatarwa yasa tafukan hannunsa ya murza idanunsa. Tare da cewa. “Wa nake gani kamar Sheykh Afif Muhammad Taj?”. Sai kuma ragowa mgnar ta tsaya a fatar bakinsa saboda, ganin yadda jama'a suka zagayeshi suna bashi hannun tare dayi mishi Barka da zuwa. Barrister Kamal kuwa sai murmushi yakeyi, saboda yana jinjinawa amintakar dake tsakanin Ishmah da Taj. Dr Nafi'u kuwa sai wani tsuke fuska yakeyi. Shi kuwa Liman da sauri ya matso kusa dasu tare da cewa Abba. “Alaji Abdullahi yau wa nake gani a masallacin mu kamar Sheykh Afif Muhammad Taj”. Fuska ɗauke da kamala Abba yace. “Ba kama bace shi ɗin nema”. Jin haka ne yasa liman ɗin saurin miƙawa Taj hannunsa suka gaisa, sai kuma ya ɗan ja baya kaɗan tare da nuna mishi gabanshi cikin alamun mubaya'a yace. “Yau nima a sahun mamu zan tsaya dan Allah, ka limamcemu”. Da sauri ya kalli limamin sai kuma yayi gaba saboda jin duk na kusa dasu na cewa. “Dan Allah ka limamcemu, kaga lokacin na tafiya”. Daga nan duk jama'ar masallacin sukabi da'ira suka tsaya a sahu tare da dai-dai ta. Shi kuwa Taj a hankali ya ɗan gyara tsayuwarsa tare da ƙara matso abun sautin, cikin sanyi murya mai cike da tawali'u ya ɗanyi gyaran murya tare da ɗan rusunar da kansa yace. “Sahhhhhhu! Sahhhhhuuuh!! Sahhhhhhhuuuuu!!!”. Yana ƙarshen sautin cike da amincin, da yasa gaba ɗaya mamun baya samun nitsuwa sit kakejin masallacin. Sai kuma ya tada iƙama tare da basmala kana karanta Fatiha da suratul Mulk, a raka'ar farko kenan ta biyu kuma Fatiha da suratul Ala. Kasancewar sallan azahar ne dole a sirrance akeyinsu yasa in banda wanda ke cikin masallacin da suka ga shigansa babu wanda yasan wake limancin. Bayan sun idar da sallan ne da sauri Abba yajasu suka tafi gida. Bayan sunyi gaishe-gashe da jajantawa juna ne, Taj ya rinƙa jero addu'o ga Dadeey. Bayan sun shafa ne, Abba yacewa ya kaishi BQ. Kanshi ya ɗan jujjuya tare da cewa. “Abba a kaini cikin gida ina son inga Ishmah”. Wani irin kallon tuhuma Dr Nafi'u ya watsa mishi ƙasa-ƙasa tare da cewa. “Kasan ana son ta samu Hutu. Ko ƙwaƙwalwarta zata motsa”. Bai kalli Dr Nafi'u Bama sai miƙewa yayi yabi bayan Adam. Barrister Kamal kuwa murmushi dake nuna nitsuwarshi yayi tare da cewa. “Dr Afif a duba min amaryata da kyau”. Juyowa yayi ya ɗan kalli Barrister Kamal sai kuma ya ɗan motsa lips inshi. “In sha Allah yanzu zatayi mgn”. Cikin tsana Dr Nafi'u yace. “Nifa Doctor ne, kuma tun randa abin ya faru take karkashin kulawata, ita dayin mgn zata iya kaiwa kwana ashirin zuwa talatin nan gaba”. Har Lau bai kulashi ba ya tafi. Suna shiga cikin Parlour, ya zauna gefen Adam dake cewa kakarsu da umominsu Hajja Umma ga Yah Taj, yanxu ya iso. Nan suka gaisa kana Adam ya miƙe tare da kallon kakar tasun yace. “Tana ɗakinta ko?”. Da sauri tace. “Eh yanzu ta shiga da mukayi salla”. Kai ya gyaɗa tare da yin gaba yana faɗin. “Bismillah Yah Taj”. Jin hakane yasa yabi bayansa. A hankali ya tura ƙofar tare da cewa. Assalamu alaikum Adda ga wani baƙo yazo miki gaisuwa. Ya ƙarashe maganar yana tura ƙofar tare da shiga. Kwance ya sameta bisa kujera 3 sitter tayi irin ƴar kwanciyar nan mai kama da kishin ƙiɗa idanuta a lunshe. Yayinda take sanye da Dubai Abaya Black collor mai masifar sulɓi da sheƙi, sai ɗan kwalinta daya zame ya faɗo bisa kafaɗunta sai gashi ta dake tubke da ya ɗan hargitse, kasan cewar numfashinta da yayi ta ɗaukewa tun randa akayi rasuwar shiyasa bata sa bra saboda tana sawa numfashi ke kuma fara yankewa, hakan ne yasa caɓɓullenta yin cirko-cirko suka tsaya cis a cikin rigar. “Bismillah ka shigo”. Adam ya faɗa yana zama bakin gadon ta. Ita kuwa Ishmah a hankali ta ɗan buɗe kwayar idanunta tare da zubasu kan ƙofar shiga kasan cewar nan take fuskanta. A hankali ya ɗan turo ƙofar tare da kutsa kai ciki. Wani......! Littafin nan dai na kuɗine ki biya ki karanta cikin aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa. mutan Niger kuma 1000fc ne rak jaka ɗaya kenan +22790899076. By *GARKUWAR MARUBUTA* [1/9, 5:51 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 9* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin nan na kuɗi ne ki biya ki karanta cikin aminci da salama 1k ne kacal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. Mutanen kasar Niger kuma 1000fc ne zaku biya jaka ɗaya kenan rak zaku ta wurin Mommy +22790899076* Wani irin maraitaccen numfashi ta fesar tare galabaitaccen yunƙura ta tashi zaune tare da zuba mishi maraitattun idunta masu cike da rauni kana murya can ƙasan maƙoshinta tace. “Taaj”. Sai kuma ta feso wani irin fitinenne numfashi daya fito daga ƙasan zuciyarta ya fito da zazzafan kukan da bata samu tayishi ba sai yanzu. Shi kuwa Taj wani tasasheshen numfashi mai cike da rauni ya fesar tare da dire kwayar idanunsa a kanta yana saurin ƙarasowa cikin ɗakin, bisa kujerar da taken ya zauna a gabanta. Cikin wani irin raunataccen kukan daya kwabce take sakin shesh-sheƙan kuka murya cike da rauni, da ɗimuwa tace. “Taj Dadeey na, ta tafi ta barni bataga aurena ba, Taj Dadeey na ta rasu banyi aureba, Taj Dadeey na ta rasu bata ganka ba ta rasu da burin ganink.” Sai kuma mgnar ta kakare saboda wani irin karkarwar da jinkinta ya farayi da wani irin fitinenne rauni daya carke mata murya ya cikashi da yanayin da mai jinta da ganinta zaiga shagwaɓarta a fili yayinda numfashi take korar juna ƙirjinta na yin sama da ƙasa dan gunjin da takeyin. Shi kam Adam sai kife kansa yayi shima yana sassayan kukan daya ingiza na Ishmah. Shi kuwa Taj ido ya zuba mata yanayi mata wani irin amintaccen kuma raunataccen kallo a yanayin da bai taɓa ganin taba, na zama irin sakewa a cikin gida kuma a ɗakinta, idanunsa da ya zuwa fuskantar zuwa kan wuyanta da ta maida kanta ta jingine bisa jikin kujerar hakan ya bawa ƙirjinta damar bayyanan da yasashi lumshe idanunsa yana mai jin tamkar ya jawota jikinsa yayi mata ruggumar da sai ya rabata da dukkan ƙuncin zuciya dana duniya ya tausashi zuciyar ta irin tausasar da sai tayi murmushi koda hawayenta basu tsaya ba. Dai-dai lokacin kuma Khadijah da Laylah suka shigo, Ganinshi ne yasa Laylah saurin zuwa gareshi tare da zubawa Ishmah ido murya na rawa tace. “Uncle Taj meyasa Aunty Ishmah take kuka”. Yana mai ɗan tallabo kanta yace. “Laylah Aunt Ishmah ta rasa mamanta, bazata sake ganintaba”. Ido na cikowa da hawaye Laylah tace. “Kamar yadda Mimina da Abbuna da Yah Irfan suka tafi, tafiya na har abada”. A hankali ya gyaɗa mata kai. Sai kuma ya kalli Hajja Umma da Aunty Hauwa da suka shigo yanzu suna faɗin. “Ishmah kiyi haƙuri ki bar kukanan, gashi Kinga kinsa ƙannenki kuka”. Suka ƙare suna nuna kallon Khadijah da Rahman da suka zauna gefen Adam suna zubda hawayen. Hannu ya ɗan ɗagawa Hajja Umma kana yace. “Barta tayi kukan”. Laylah kuwa da sauri ta matsa kusa da Ishmah tare da faɗawa kan cinyarta ta ruggume tare da sakin kuka. Hakan ne yasa Aunty Hauwa zubda hawayen domin tasan tarihin maraicin Laylah. A tare suka fita ita da Hajja Umma. Yayinda Adam dasu Khadijah ke biye dasu a baya. Ya rage daga shi sai Ishmah da Laylah. Shiru yayi ya rumtse idanunsa yana jin sautin kukanta na ratsa kunnuwansa da zuciyarsa, wani irin tsuma jikinsa keyi tamkar wanda zazzaɓi zai rufe da ƙarfi ya taune lip inshi na ƙasa domin jin yana gab da gaza yin control ɗin jikinsa da zuciyarsa dan ji yake zaifa jawota jikinsa. A hankali ya buɗe idanunsa jin Laylah na cewa. “Aunty Ishmah kiyi haƙuri, in sha Allah Dadeey na cikin dausayin aljanna, ki daina mata kuka, Uncle Taj yace min ba kyau nayiwa mamaci kuka, Aunty Ishmah kinga na dena yiwa Mimina da Abba na da Yah irfan kuka, dan Uncle Taj yace min wannan shine jarrabawata in bayi butulciba Allah ya bani ladan yarda da ƙaddara. Kema kada ki butulcewa kaddararki kiyi haƙuri ki daina kuka, ke gashi ma Abbanki yana raye gasu Mahmud ga kuma Uncle Taj yana sonki”. Cikin zubda hawayen tare da kiciniyar danne shesh-sheƙan kukanta ta ɗan ɗago kanta tare da zira mishi rikitattun idanunta. Sai kuma duk suka kalli Laylah jin ta kamo hannun Taj ɗin tare da jawoshi ta nufi fuskar Ishmah tana magana cikin rawan murya tace. “Uncle Taj ka share mata hawayenta kace ta daina kuka, kace mata kana sonta ina sonta Addawa na sonta Bama son tayi kuka”. Ta dire mgnar idonta na zubda hawayen kana murya na rawa. Sassayan numfashi ya fesar tare da jingina bayan shi da kujera sai kuma ya ɗan janye hannunsa daga riƙon da Laylah tayi mishi sai kuma ya ɗan gyara zamansa a hankali ya ɗan sa babbar yatsarsa kan lips inta da take ta ciccijewa dan ta samu ta tsaida kukanta yatsarsa yasa kan lips in tare da ɗan janye su sai kuma yasa yatsar tsakanin haƙoranta. Sai kuma duk suka kalli juna jin Laylah na cewa. “Uncle Taj kace muna sonta kaima kana sonta ka ɗauke mana ita mu tafi da ita, Ummeey zatace tana sonta kuma kaima kana sonta ko”. Kanshi ya ɗan jinjina mata. murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Duk da ban san ya akeji ba in an rasa makusanta, Amman ina jin ciwo cikin zuciyata irin ciwon da ban taɓa jin irinsa ba, inajin zuciyata tayi min ƙunci irin ƙuncin da bazan iya kamantashi ba, kukanki yana sa inji tamkar raina ake zarewa, na hana Hajja Umma ta hanaki kuka ne saboda nasan zai rage Miki raɗaɗin zuciya. Amman kukan yayi yawa yana azabtar da zuciyata Please dan Allah Ishmah kiyi haƙuri ki daina kuka, ki gafa Laylah yarinya ƙarama Allah yayi mata Jarrabawar data ninka taki ciwo, an kashe mata, Uwa, Uba, ɗan uwa, ƴar uwa, maƙotansu, kai duk dangintafa yanzu bata da kowa a duniya sai ni dake da nake son mu zame mata uwa da uba da ƴan uwanmu da nake so su zame mata ƴan uwa. Kiji me take ce miki ke ai kinji daɗi ga Abbanki, kuma Uncle Taj yana sonku, ki buɗe ido ki ki kalleta fa. Just 11 years ne da ita.” Cikin sanyi ta buɗe idanunta tare da fara sauƙe tagwayen ajiyan zuciya. Dai-dai lokacin Hafsah ta shigo da tray a hannunta wanda ke ɗauke da plate ɗin fruits sai goran ruwa da kwalin Juice. Bisa stoll ɗin dake gabansa ta ajiye trayn kana ta juya ta fita. Gorar ruwan ya ɗauka tare da ɓalle marfin kana ya zuba mata a cup ɗin tare da miƙa mata. “Amshi kisha”. Cikin sakin wani nannauyan ajiyan zuciya ta tsuke lips inta tare da marairaitar da kwayar idanunta cikin sakin sassayan kuka murya cike da rauni da yake bayyana shogwaɓarta tace. “Taj shike nan yanzu bani da uwa a duniya na zama marainiya ba uwa ba miji”. Haka nan yake jin bazai iya janye idanunsa cikin nataba yadda tayi da fuskantar kai kace ƴar 8 yaers ce. Ƙara miƙo mata cup ɗin yayi tare da lumshe rikitattun idanunsa murya a sarƙafe da tausayi da zazzafan yanayi a kanta cikin sanyi yace. “Ishmah duk biyu Taj ɗinki zai cike miki gurminsu dan bazai bari ki zubda hawayen kiba, amshi ruwa kisha”. Cikin sanyi ta amshi cup ɗin tare da tsaida idanunta da suka sauya launi saboda rashin bacci da kukan data tayi yanzu, manyan idanunsa da tausayinta ya sauya musu launi ya lunshe matare da mata alam sha. Cup ɗin ta kai bakinta, tare da zuƙan sassayan ruwa, idanutan ta lumshe lokacin da taji sanyin ruwan yana ratsa maƙoshinta tare da dira kan zuciyarta. “Hhyyymmm”. Ta ajiye wani numfashin dai-dai lokacin kuma Hafsat ta shigo da wani tray ɗin, wanda ke ɗauke da ƴar madaidaiciyar kwarya mai masifar kyau, sai kuma ludeyin duba, da kuma wata ƴar roba, ajiyewa tayi gefen na forkon tare da cewa. “Bismillah Yah Taj kasha ruwa, kafin in kawo ma abinci”. Da sauri ya kalli trayn duka biyu, kana ya kalleta cikin mamaki yace. “Wani abincin kuma, a'a karma ki kawo wani abu, wannan ma ai ya isa”. Ɗan murmushi tayi tare da cewa. “A'a Yah Taj ai wannan duk ba abinci a ciki ɗan abubuwan shane kawai”. Yana mai kallon Laylah dake ƙwaƙume da Ishmah yace. “Eh ya isa, ki huta”. Kai kawai Hafsat ta gyaɗa dan ta rabu dashi, tana fita ta wuce, part ɗin Yah Muhammad, kai tsaye kitchen ta wuce nan ta samu Aunty Nana sukaci gaba da aikinsu. Ita kuwa Ishmah cikin sanyi murya a disashe harce raunace tace. “Taj kasha ruwa!”. Kai ya jujjuya mata, cikin sanyi hawaye na zuba tace. “Meyasa zakace bazaka sha ruwan ba?”. Fuskarta ya nuna tare da cewa. “In dai har ina ganin hawayenki na kwaranya na gaza tsaidasu, to me amfanin zuwana, kuma ya zanyi in iya shan wani abu a bakina daya gaza tausar zuciyarki Ishmah”. Ya ƙare maganar da iya gskyar zuciyarsa. Da sauri ta fara sharce hawayenta da bayan hannunta tare da karkata tana ɗan gyara zamanta ta fuskanceshi da kyau tana mai ɗan ture Laylah kaɗan ta zauna a tsakiyarsu cikin muryar da tafi kama data sakalallu da yarinya tace. “Ka gani na share hawaye na, kuma yi shiru, Please kasha ruwa”. Idanunsa ya ɗan siranta tare da cewa. “Ki fara ci!”. Da sauri ta jawo, stoll ɗin gabanta, plate ɗin dake ɗauke da fruits ta ɗauka, tare da ɗan matsowa kana ta ajiye shi kan sawun Laylah dake miƙe a tsakiyarsu, fork ɗin ta ɗauka tare da miƙa mishi, shiru yayi yana lallonta ta tsakankanin gashin idonsa yayinda zuciyarsa da ruhinsa ke haƙaito mishi wani irin amintaccen alaƙa a tsakaninsu duk duniya banda Ummeey da Addawa ko yayunshi baya irin wannan kusanci dasu gwarama Aunty Rashida. ɗaya fork ɗin ta sake ɗauka tare da ɗan sokashi saman water millo, sai kuma ta bawa Laylah tare da cewa. “Hah Laylah buɗe baki”. Ciki Laylah ta shafa tare da cewa. “Alhamdulillah Aunty Khadijah ta bani Labal, da wani abu mai daɗi a ciki nasha cikina ya cika. Uncle Taj ne baici komaiba tunda muka taso”. Ta ƙare maganar da alamun fura da nonon da tasha ya fara sakar mata kasalan bacci. “Ki ƙara da fruits ɗin mana“. Kai ta jujjuya tare da ɗan lumshe idanunta kana ta ɗan raɓa jikin Ishmah ta mannu da ita. Ganin haka ne yasa ta ɗan tallabeta ta gefe, sai kuma ta tsaida idonta kan fuskar Taj ɗin tare da bashi fork ɗin kana ta kwaɓe fuska tare da cewa. “Dan Allah kaci”. Ta ƙare maganar hawaye na taruwar mata, ganin haka ne yasashi amsar fork ɗin. Yanka uku yaci na kankanan, sai kuma ya ɗan soki Apple yaci kusan rabinsa kana ya ɗan ture plate ɗin tare da cewa. “Alhamdulillah”. Kai ta ɗan jinjina kana ta ɗan sunkuyo ta buɗe ƴar kwaryar nan, damemmen fura da nono ne, mai ɗan karen sanyi ya damu yayi luƙui. Sai kuma ta buɗe ƴar robar nan, gogeggiyar kwakwace sai kuma ƴan yanka-yanka inabi. Numfashi ta ɗan fesar tare da juyesu cikin nonon. tare da ɗan sa ludeyin nan ta motsashi ya haɗe da juna. Sai kuma ta daukeshi daga ƙasansa wanda fayfayne da zagayyen abin aje ƙoren, bisa cinyarta ta ɗaurashi tare da matsoshi sosai, tana ajiye ludeyin ta gabansa tace. “Bismillah.” Rau-rau tayi da ido alamun zatayi kuka ganin ya kafeta da ido yaƙi cewa komai. Ganin yadda tayin ne ya sashi ɗaukar ludeyen tare da ɗan ɗiba. Sai kuma ya kaishi bakinta yana faɗin. “Ce Bismillah”. Rau-rau tayi da idonta tare da cewa. “Bana jin yunwa”. Ta ida mgnar hawayenta na silalowa. Lumshe idanunsa yayi kana ya buɗesu tare da tsareta dasu yana mai ƙara yarda da zuciyarsa cewa halittartace shagwaɓarta dake kashe mushi zuciya da sashi cin ruwan ƙanshi na ƙafwa cikin sanyi tamkar raɗa yace. “In baki shaba bazan shaba”. Ya ida mgnar yana manna mata ludayin bisa lips inta. Tare da mata alamun sha. Cikin jin bata sha'awar cin komai na duniya ta ɗan buɗe bakin, a hankali ya juye mata furar a baki kana ya ɗan janye ludayin. ita kuwa Ishmah hankali ta maida lips inta ta rufe ba tare da ta haɗiye samunba. Da sauri ta ɗan fiddo idanunta ganin ya ronƙofo ya matso da kanshi saitin fuskantar. Wani irin tsuma jikinta ya fara na kusancinsu. Shi kuwa Taj a hankali ya haɗe laɓɓansa ya ɗan hura mata iskar bakinsa kan fuskar wanda yasata jan numfashi da yafi kama da ajiyar zuciya kuma dole ta haɗiye damun furar. A tare suka sauƙe numfashi kana yasa hannun da niya ɗibo wani sai kuma yayi saurin ɗago kanshi jin ta cewa. “Dan Allah ka sha, ai na sha kuma wlh bana jin yunwa”. Ta ƙare maganar tare da amsar ludeyen ta ɗebo ta miƙa mishi. Amsar ludeyen yayi tare da yin Bismillah. Wani irin sassayan numfashi ya fesar haɗi da lunshe idanunsa lokacin da yakai samun bakinsa yaji ɗan-ɗanon nonon gami da garɗin fura, kana ga garɗin kwakwa da inabi, ga zakin zuma a madadin sugar. Tongue ɗinsa ya ɗan zaro tare da ɗan lasar gefen lip inshi na sama da nonon ya ɗan taɓa. Ido ta ɗan zubawa sajenshi dake zuba ƙelli da sheƙi. Shi kuma Taj cikin jin daɗi damun, yaci gaba da shan. Sosai ya sha kusan rabinsa, kana a hankali yasa hannunsa ya ɗauki fefeyin da aka rufe dashi, tare da rufewa tare da cewa. “Alhamdulillah Ishmah yanzu dai na ƙoshi, ki ajiye minshi a fridge gobe zan sha”. Tana mai ɗan tallabo Laylah sosai a jikinta tace. “Yayi ma daɗi”. Kai ya ɗan jinjina mata tare da miƙewa tsaye jin an kira sallan la'asar. “Zaka tafi masallaci ko?”. Yana mai gyara tsayuwarsa yace. “Eh ki tada Laylah ma kuyi salla”. Tana mai gyarawa Laylah kwanciya tace. “Toh”. Sai kuma tabi bayan shi suka fito. “Ishmah kin fito”. Hajja Umma dake zaune da Khadijah tace. Cikin sanyi murya tace. “Eh”. Da sauri duk suka juyo suna kallonta dai-dai lokacin kuma Abba da Barrister Kamal, da Dr Nafi'u, suka shigo Mukhtar na baya. “Wa alaikissalam”. ta amsa Cikin jin daɗi Abba da Yayunta suka haɗa baki wurin cewa. “Ikon Allah Aisha baki ya buɗu”. Suka ƙare maganar suna shigowa tare da yiwa sauran iso. Ido ta zubawa Mukhtar Bappa Kawu kenan kamar yadda ƴaƴan yayunsa da ƙannensa ke kiransa. Shima ido yan zuba mata cikin so da tausayin maraicin daya cimmata a gida batayi aureba. “Bappa Kawu kazone”. Kai ya ɗan sunkuyar domin tunda batun soyayyarsu ta watse ta koma kiransa da Bappa Kawu. Sai kuma ta kalli Barrister Kamal dake cewa. “Hajia ta, ya ƙarin haƙurinmu?”. Kai ta ɗan sunkuyar hawaye na silalomata tace. “Alhamdulillah Barrister haƙuri ya zama dole”. Dr Nafi'u kuwa gefentan ya matso sosai tare da cewa. “My wife ya jikin da sauƙi ko”. Kai ta gyaɗa mishi alamun eh saboda yadda ya matsota har kamar zai manne kafaɗarsa da tata. Barrister Kamal kuwa Taj ya kalla cikin sonshi yace. “Kaji manyan likitocin zuciya da ƙwaƙwalwa ita da akace sai bayan kwana 20 zatayi mgana sai gashi in 20 minute ka sa bakinta buɗewa. Anya kuwa Sheykh ba wani sirri tsakaninku”. Kusan duk Murmushi sukeyi tare da kallon Taj ɗin da ya ɗan kalli Ishmah tare da cewa. “Ba wani sirri Barrister haɗin Allah ne”. Dr Nafi'u kuwa tauke fuska yayi yana dannawa Taj ɗin harara. Ita kuwa Ishmah Taj ɗin take kallo yadda yake kauda kai baya ma son kallon Dr Nafi'u. Sai kuma ta kalli Mukhtar dake cewa. “Boɗɗi am, ya mukaji da hakuri?”. Ya ƙare maganar hawaye na tsatstsapo mishi, domin sosai ya saba da Dadeey ya kuma san taso alaƙarshi da ɗiyarta, yana kiranta da Boɗɗi ne kamar yadda Dadeey ke kiranta. A hankali ta ɗan sa hannunta share hawayenta tare da zama kusa da Hajja Umma, murya na rawa tace. “Haƙuri ya zama dole Bappa Kawu, Dadeey na ta tafi”. Sai kuma ta fara shesh-sheƙan kuka, cikin sanyi murya mai cike da tausasawa da kuma kulawaTaj yace. “Ishmah kiyi haƙuri, mu bar yiwa Dadeey kuka muyi mata addu'a ko, bana son kukan nan ya isa haka”. Ya ƙare maganar yana zama gefen Barrister Kamal. Ita kuwa Ishmah ta ƙasan ido take kallon Barrister Kamal, Dr Nafi'u, Mukhtar, in manema ne dai da masoya Allah bai hanataba, auren nedai Allah bai sauƙo da shiba. Shi kuwa Taj ɗan gyaran murya yayi tare da fara jawo addu'o'in newa mamaci gafara da yafiyar Allah da kuma rahamarka. اللَّهُمَّ اغْفِرْ لَهُ وَارْحَمْهُ، وَعَافِهِ، وَاعْفُ عَنْهُ، وَأَكْرِمْ نُزُلَهُ، وَوَسِّعْ مُدْخَلَهُ، وَاغْسِلْهُ بِالْمَاءِ وَالثَّلْجِ وَالْبَرَدْ، وَنَقِّهِ مِنَ الْخَطَايَا كَما نَقَّيْتَ الثَّوْبُ الأَبْيَضَ مِنَ الدَّنَسِ، وَأَبْدِلْهُ دَاراً خَيْراً مِنْ دَارِهِ، وَأَهْلاً خَيْراً مِنْ أَهْلِهِ، وَزَوْجاً خَيْراً مِنْ زَوْجِهِ، وَأَدْخِلْهُ الْجَنَّةَ، وَأَعِذْهُ مِنْ عَذَابِ الْقَبْرِ وَعَذَابِ النَّارِ Kusan a tare duk suka lumshe idanunsu harda shi kanshi Dr Nafi'u. Domin yadda yake jan sautin addu'ar da yadda muryarsa ke fitane yasa su jin tsikar jikinsu na tashi. Kusan a tare a tare suke amsawa da Amin-Amin. Bayan su shafane kuma, suka miƙa dan fita, har sunje bakin ƙofar Mukhtar yace. “Baddi ni zan wuce in munyi salla, sai munyi waya”. Cikin sanyi tace. “Ngd ƙwarai Bappa Kawu ka gaida mutan Gombe, Allah ya maida ka lfy ka gaida min Sadik da Aliya”. Cikin jin daɗi yadda take son ƴaranshi yace. “In sha Allah zasuji”. Daga nan suka fita. Bayan an idar da sallan la'asar ɗin ne Ishmah tacewa. Khadijah da Hafsat suje su Gyara BQ. “Ai tun ɗazu Rahman da Minat suka gyara shi komai fes kin san Rahman gwanar gyara ce”. Cewar Khadijah, cikin gamsuwa tace. “To muyi salla”... Da daddare bayan anyi sallan Isha. Kusan duk tare suke a Parlour Dadeey a nan kuma sukaci abincin daren. Sai shi da Rahama ta kai mishi BQ ɗin. Washe gari da safe misalin ƙarfe 10 dai-dai Ishmah ta fito daga cikin gidan ta nufi BQ ɗin tana riƙe da hannun Laylah. Khalid da Minat na biye dasu a baya, riƙe womers. Ahankali ta ɗaga hannunta na dama tayi Knowking kusan sekonni talatin taji shiru sake knowking tayi har sau biyu still taji shiru ɗan jimm tayi tare da ɗan fesar da sassayan numfashi kana ta sake knowking a karo na uku, still shiru taji alamar ba motsin mutum da zai buɗe ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta ɗan murɗa Handle ɗin ƙofar lumshe idanunta tayi tare da ɗan buɗesu jin ƙofar a abuɗe take. Turawa tayi ta kutsa kanta ciki, bakinta na ɗauke da sallama a nitse ta sanya ƙafarta na dama acikin Falon ahankali ta saki wani sanyayyan numfashi tare da shaƙan wani ni'imantaccen ƙamshi mai daɗin shaƙa haɗi da sanyin Ac mai sauƙar da nitsuwa daya wadataci cikin Falon. Ahankali ta ƙara sa takawa cikin Falon yayin da sanyin ke ratsa mata Jiki da zuciya. Minat, Khalid .ke biye da ita kai tsaye suka nufi dining area. Iska mai sanyi ta fesar tare da tsayawa tsakiyar falon tana mai karewa ko ina kallon tsaf-tsaf gwanin ban sha'awa komai neat-neat a ranta tace kai Masha Allah Rahamah ba dai tsafta ba komai na falon ya gyaru sai ɗaukar ido da ƙyalli yake ga wani masifeffen ƙamshi dake tashi wasu irin kujeru ledar Set ne Neavy blue sai tangamemen TV da Tv starm da Woofer dake gefe tsakiyar falon kuwa wani Turkey Carpet na Neavy blue da ratsin fari yayin da cotton ɗin ma suka kasance Neavy blue da ratsin fari sosai falon yayi kyau na fitar hankali. Cikin lumshe Idanu ta sauƙe ajiyar zuciya mai sanyi kana ta juya gefen dining, idanunta suka sauƙa akan, Warmers, Flaks, Mug, da sauran abubuwan buƙata wanda bisa dukkan alamu ba'a ataɓa su bama. Ɗan ware manyan Idanunta tayi kana aranta tace. “Kenan beyi breakfast ba har yanzu?”. Cikin yanayin nutsuwarta da kuma sanyi data sakeyi ta juya ta kalli ƙofar bedroom ɗin dake gefen dama kasancewar BQ ɗin 2bedroom ke ɗauke dashi shiru taji ɗakin alamar ba kowa, ɗan juyawa tayi tare da maida idanunta ɗakin gefen hagu nan ma taji alamar ba kowa sake juyawa tayi zuwa ɗakin gefen dama jin kamar ana magana ahankali ta zubawa ƙofar ido. Cike da nutsuwa daya gama ratsa sassan jiki da tsoka da jini dake bin baki ɗaya ilahirin jikinsa saboda darajar Alqur'ani mai girma da yake kansa a hankali ya murɗa Handle ɗin ƙofar ya fito. Cikin sanyi Ishmah ta ƙyafta Idanunta sau biyu kana ta tsai dashi akansa ganin sa sanye cikin riga da wando na kafta Milk color da aka watsa masa ɗinki irin na matasan zamani masu nutsuwa da arziƙi yayin da kansa ke sanye cikin hula coffee da rastin Milk kana ƙafafunsa na sanye cikin wasu takalma coffe da ratsin milk Bertozzi mai masifar taushi da ƙyalli wanda bazai gaza kaiwa 85k ba sai wani irin ni'imtaccen ƙanshin yake zubawa. Ahankali ta sake ɗagowa tun daga kan rumfar ƙafarsa har zuwa kan kyakkyawar fuskarsa dake ɗauke da saje dake wani irin ƙyalli da sheƙi haka nan ta kasa ɗauke idanunta akansa. Aɓangaren.Taj kuwa hankali shima ya zuba mata manyan Idanunsa Masu masifar haske da sheƙi kana suna ɗauke da zara-zaran eyelashes sanye take cikin riga da skirt na atamfa Golden Color da ratsin light blue da ratsin Orange atamfar ta zauna ɗass ajikinta haka zalika Skirt ɗin ma ya zauna ɗass kana gyalen da ta yane kanta zuwa kafadarta shima light blue ne yayin da jikinta ke fitar da sihirtaccen ƙamshin Humra da Kwallaccar da Garkuwa ta bata tayi masifar kyau duk da cewa ta ɗan rame kana ga idanunta da suka kumbura wanda bisa duk kan alamu tayi kuka sosai duba da yanda Idanunta sukayi luhu-luhu dasu cikin nutsuwa dake ratsa sassan jikinsa ya fara takowa ahankali batare daya janye idanunsa dake cikin nata ba haka zalika itama bata janye idanunta daga nasa ba. Ahankali Minat ta juya ta kallesa bayan ta ajiye Warmers ɗin akan dining kana ta ratsa gefensa tace. “Uncle Taj ina kwana”. Cikin fesar da numfashi yace. “Lafiya lau my Daughter ya gida”. Ya amsa batare daya janye Idanunsa daga kan Ishmah ba. Gefensa Khalid ya matso tare da faɗin. “Ina kwana Uncle Taj”. Ahankali ya ɗaura hannunsa kana Khalid still Idanunsa na cikin na Ishmah yace. “Lafiya lau My Boy ykk?”. Murmushi Khalid yayi cikin jin daɗin yanda yake kiransa da My Boy tare da cewa. “Lafiya lau”. Kana cikin nutsuwa da takun kamala ya cigaba da tafiya. Ishmah kuwa har zuwa lokacin tana riƙe da hannun Laylah. Laylah kuwa murmushi tayi tare da cewa. “Uncle Taj”. “Na'am Laylah ”. Ya amsa batare daya iya cire idanunsa daga kan Ishmah ba”. Cike da farin ciki tace. “Uncle Taj kalli kayan da Aunty Ishmah ta ɗinka min ya min kyau ko Uncle Taj??”. Murmushin gefen baki yayi wanda ke sake fitar da ainihin fuskarsa, kanshi ya gyaɗa mata duk da cewa bai kalleta ba amma yace. “Masha Allah kinyi kyau sosai Laylah Aunty Ishmah ta iya zaɓi ta zaɓawa Laylah kayan daya dace da ita”. Cikin farin ciki Laylah ta sake kallon kayan da sukayi mata kyau tamkar dan ita aka halicci Les ɗin tare da faɗin. “Ta ɗin ka min da yawa akwai wasu ma acikin gida”. Still Idanunsa na cikin na Ishmah ya gyada kai kana yace. “Ta kyauta mun gode”. Akuma dai-dai lokacin ya ƙara sa daf da ita kamar zai gogi jikinta har zuwa lokacin sun gaza janye Idanunsu acikin na juna ahankali yake mirza ƙaramar wayarsa dake cikin hannunsa yayin da ɗaya wayar ke maƙale akunnensa. Kana adaidai lokacin kuma na wayar ke cewa. ”Hello Afif”. Bisa duk kan alamu murya ce na ɗaya daga cikin Sanannun Malaman mu na nan gida Nigeria ne. Jujjuya ƙwayar idanunsa yayi kasancewar baki ɗaya hankalin da baya kan wayar sai kuma yaji wayarma ta katse baki ɗaya. Cirota yayi daga kunnensa ya zura a aljihun gaban rigarsa ƙaramar wayar ya juya kana ya kai wayar kan kumatun Ishmah ya lakata cikin sanyin murya mai haɗe da taushi yace. “Wannan kallon fa? Duka na menene?”. Sai alokacin ta saki sanyayyan numfashi tare da lumshe Idanunta na ƴan sekonni kafin ta sake buɗe su akansa kana ta ɗan ja baya tare da cewa. _“Fatabarakallahu Fii Ahsanul Khaliƙin”_. Murmushi yayi tare da kallonta sama da ƙasa kana yace. _“Masha Allah Fatabarakallahu Fii Ahsanul khaliƙin”_. Kallonsa tayi kana ta kau da kai tana wasa da yatsun hannunta tace. “Kaga yanda kayan Hausa Fulani suka yi maka kyau ajikinka? zanso in ganka cikin babbar riga, ka kuwa ga yanda kayi kyau Tajjjj?”. Ta ƙarashe kiran sunansa cikin wani salo na musamman, domin Allah ya sani tana bala'in son sunansa”. Murmushi yayi wanda ya bayyanar da fararen haƙoransa yayi kana ya juya ya kalleta tare da faɗin. “Saboda komai namu iri ɗaya shiyasa kika iya fahimtar collors ɗin da nake so, da Abinda zai karɓeni da kuma abinda zai zauna ajikina, Nayi mamaki sosai jiya da daddare da Adam ya kawo min kayan, nayi ta mamaki da duka kayan sukayi dai-dai da jikina ban matsuba basu min yadda ɗinkunan ƙasarmu sukeyi ba masu faɗi” Sai kuma ya ɗan fesar da wani irin numfashi mai cike da tarin Manufofi gami da ma'anonin da shi kaɗai ya sani sai kuma Allah. A hankali ya ɗan motsa lips inshi ya cigaba da cewa. “Nasan cewa baki taɓa tambaya size na ba amma bansan ya akayi kika san size ɗin takalmina ba duk takalman da kika siya min sunyi daidai da ƙafana ban sani ba ko tef kika samu akaro na farko da muka haɗu kika gwada”. Ɗan ware idanunta tayi tare da sakin murmushi jin abinda yace. Shi kuwa cikin gaskiya da gaskiya ya cigaba da faɗin. “Hatta hulunan da kika siya sunyi dai-dai da kaina, hakama Boxers da singlet Why Ishmah ya akayi haka?”. Da sauri ta janye idanunta daga nashi cike da kunya, haka kawai taji tsikar jikinta na tashi saboda yanda yaja maganar can ƙasan maƙoshi da kuma wani abun da take hangowa cikin ƙwayar idanunsa. Cikin fesar da numfashi da wani irin yanayi na musamman dake ratsata sassan jikinta aduk sanda taji sautin muryan sa ta narkan da ƙwayar idanunta tace. “Yadda komanmu ke kasance wa irin ɗaya haka tunanin zuciyar mu ma iri ɗaya may be shitasa na iya fahimtar abinda zai maka dai-dai aranka kuma dama nasani cewa abinda ya min kyau zai maka kyau”. Kallonta yayi yana mai jin nutsuwarsa na barin jikinsa har ya fara gaza control ɗin kansa, a hankali ya matsa gefenta tare dasa waya ya lakace mata hanci yace. “Wannan haka yake, kuma in dai in a zaɓine ke ba baya bace in dai kika zaɓi abu, toh abin na musamman ne ba wanda zai iya kushewa”. Lallausan murmushi ta saki tana mai jin farin cikin yadda ya yabi zaɓinta kana tace. “Ai kaima na musamman ne shiyasa komai naka ya kasance na musamman”. Ta ƙarashe Maganar tana nuna masa hanyar dining tare da cewa. “Bismillah Taj kana son kabar kanka da yunwa kalan ka koma Ummey tace shalelenta ya rame a Nigeria”. Ɗan ware idanunsa yayi kana yace. “Saboda me?”. Agogon hannunta ta duba kana ta langwaɓar da kanta tare da cewa. “Ganifa kusan 11:00 Am bakayi breakfasts ba gashi har na haɗama lunch”. Ta ƙarashe Maganar tana taka kan step ɗin dining area yayin da yake biye da ita. Yaran kuwa a tsakiyar falon suka zabe suna kallon hotuna awayar Ishmah dake hannun Laylah. Taj kuwa cikin lumshe Idanu yace. “Wa yace Miki banci abinci ba? Tun da muka dawo daga Masallaci Sallar Asbah Abba ya kaini Falonsa ke kina can kina bacci nasha tea tare da Abba sannan kuma naci gashi mai ɗumi bana tare da yunwa shiyasa”. Ɗan ware idanunta tayi tana Murmushi shi kuwa cikin jin daɗin kulawar da take basa ya cigaba da cewa. “Naje mun gaisa da Hajja Umma kina can kina bacci zasu ta dake nace su barki kiyi baccinki”. Murmushi tayi kana tace. “Uyummm Sai karfe goma na tashi nace bari na maka ɗan abu mai sauƙi. Kaci abincin da nayi maka da hannuna”. Sanyayyan numfashi ya fesar tare da faɗin. “Masha Allah Nagode sosai kuwa”. Ya ƙareshe maganar yana zama akan dining. Kana itama ta zauna tare da buɗe Warmers ɗin dake farko wanda ɗauke da Gashin kifi tarwaɗane da yaji Vegetables aka zagayesa da source sai kuma Cous-cous da tayi Jollof ɗin sa wanda shima yaji Vegetables a plate ta zuba kana tasa ka masa kifi agefe spoon tasa tare da janyo Mug ta haɗa masa tea ta ajiye gefensa tana mai sakar masa guntun Murmushi dake nuna har lau ƙuncin zuciyar rashin mahaifiyarta na tare da ita, sai danneshi da takeyin da tawakalli tace. “Taj Bismillah”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Toh matso muci”. Kai ta girgiza tana gyara zaman Flaks ɗin tace. “Aini naci nawa kaine nake muradin inga kaci”. Ta ƙare maganar cikin yin ƙasa da idanutan sabida ganin wani irin kallon da yake binta dashi, kallon da ta gaza fahimtar na menene. Shi kuwa Taj cikin sanyi ya motsa lips inshi yace. “Ok”. Ya faɗa tare da ɗan matsowa alamar zai fara ci sai kuma ya kalleta jin tana cewa. “Dawa kake yin waya?”. Idanu ya jujjuya kana yace. “Ina waya da Sheiky Isa Ali Pantami”. Kai ta gyaɗa tare da faɗin. “Masha Allah kace da Manyan Mutane kake waya”. Yana kai spoon ɗin bakinsa yace. “Eh saboda munyi dashi idan na zo zamu haɗu sannan zan wuce Maiduguri akwai masallacin juma'a da nayi musu al'ƙwarin zan limamcemu sallan jumma'a, sannan kuma zanje Zamfara akwai masallacin da zan buɗe nayi musu alƙwarin za'a buɗe dani, yanzu kuma Sheykh yace zamuje Kano da Bauchi tare dashi”. Da sauri ta zare idanunta sai kuma ta langwaɓar da kanta tace. “Toh rabuwa biyu zakayi?”. Kai ya jujjuya tare da cewa. “Baxan rabu biyu ba amma dole zan bawa ɗaya daga ciki haƙuri zanje na Borno jumma'ar nan, sannan kuma na Zamfara zanje in jasu Khamsus Salawat na rana ɗaya daga nan in wuce Kano nan zanmuyi zama da su Sheykh Aminu Daurawa”. Rau-rau da Idanunta tayi kana tace. “Kenan tafiya zakayi?”. Kallonta yayi tare da langwaɓar da kansa kana ya zura mata idanunsa yana mai jin wani abu na dukan zuciyarsa murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Bakyaso in tafi ne?”. Numfashi taja kana ta langwaɓar da kanta ta zuba masa Idanu batare da tace komai ba. Cikin tausasa murya yace. “Baki ban amsa ba bakyaso in tafi ne?”. Still shiru tayi amma aranta da zuciyarta tana jin kamar shine farin cikinta ganinsa ya sanyata cikin maɗaukakin farin cikin wanda ya gusar mata da kaso 70 cikin 100 na damuwarta tana ji kamar su dawwama ahaka kai ta girgiza alamar ba haka bane. Cikin fesar da numfashi ya janye idanunsa acikin nata tare da faɗin. “Kuma zanje Abuja zamu haɗu da Shugaban izala na ƙasa baki ɗaya”. Ahankali ta saki nannauyan numfashi kana tace. “Hmmm?”. Shi kuwa Taj a hankali ya kai tsokar kifin dake haɗe da Vegetables da ɗan Arish bakinsa, lumshe idanunsa yayi tare da buɗesu a lokaci guda, saboda ɗanɗanon girkin daya game mishi baki. Hannunsa na hagu ya ɗan dungule tare da yi mata alamar jinjina ya haɗe babbar yatsarsa da manuniya. “Masha Allah Ashe Boɗɗi Daddy ta iya girki ovar kinci in baki 99.” Murmushin jin daɗi tayi tare da cewa. “Nagode”. Sai kuma ta ɗan kwaɓe fuska tare da cewa. “Uhmmm”. Yana shafa yalwataccen sajensa dake ƙyalli yace. “Menenr faɗi mana”. Kanta ta sunkuyar ƙasa sai kuma ta ɗago ahankali tace. “Ai dai wannan lokaci nane zuwanmu ne kayi ko?”. Kai ya gyaɗa cikin tabbarwa yace. “Eh zuwanki ne albarkacinki sukaci kuma Al'farman abinda suka nema yana da nauyi bazan iya ƙin yi musu ba saboda manyan mutanene masu daraja, Amman duk da haka in bakya son inje sai mu basu haƙuri ko”. Kai ta gyaɗa tana mai jin wani irin abu da yafi kama da kewa tace. “A'a kaje”. “Yauwa Bestie haka nake son ji”. Ya faɗi yana mai ci gaba da cin abincin tare da ɗan kurban tea ɗin. Cikin sauri tace. “Amman ai zaka dawo ta nan kafin ka tafi ko”. Yana ajiye mug ɗin tea ɗin yace. “Ba dole ba, ai dole in dawo nan, sai randa zan bar ƙasar zanbi jirgin safe in koma Abuja, da dare mu tashi”. Cikin sanyi tace. “To Allah ya yarda”. Amin yace tare da gyara zaman yace. “Jiya da daddare bayan munyi Sallar Isha'i mun dawo falon Abba Ummeyna da Yah Abana da Addawa duk sun gaisa dasu Abba da Yah Muhammad har Khadijah da Hafsat ke kina bacci yanzu bari na kira su ku gaisa”. Kai ta gyaɗa tare da faɗin. “Toh ba laifi amma yanzu dai ka karasa cin abinci tukunna”. Kallonta yayi kana ya ida zaro wayar daga aljihunsa yace. “Um bari na kirata tukunna kuna wayar ina cin abinci”. Kai ta gyaɗa kana shikuma ya kira Ummey tana ɗagawa tace. “Ya dai Babana ya Nigeria?”. Cikin nutsuwa da girmama wa yace. “Alhamdulillah Ummey Nigeria akwai daɗi”. “Masha Allah ina Ishmah”. Kallon Ishmah da itama shi take kallo yayi kana yace. “Gata nan ma bari in bata ku gaisa”. Ummey na gyara zaman wayar akunnenta tace. “Toh bari in mun gaisa in bawa Malam su gaisa dan muna tare”. “Ok toh shikenan” ya faɗa yana bawa Ishmah wayar amsa tayi kana suka gaisa cikin mutumtaka da nutsuwa tace. “Ummey ina kwana”. Cikin jin tausayinta Ummey tace. “Lafiya lau Mamana ya ƙarin haƙuri?”. Idanunta na kan dining ɗin tace. “Alhamdulillah haƙuri ya zama dole”. “Toh Allah yajiƙanta da Rahama ga Malam”. Amsa malam tayi kana yace. “Aysha”. Cikin nutsuwa ta risinar da kanta tare da cewa. “Na'am Yah Abana ina kwana”. Amsawa yayi yana mai jin daɗin sunan data kirashi dashi sunan da kenan daga Taj sai ita kaɗai ke kiransa dashi amsawa yayi cikin kulawa, kana yayi wa Dadaynta addu'oi masu yawa wanda yasa taji nitsuwa kana bayan ya gama ta miƙawa Taj wayar amsa yayi yana kai Spoon ɗin daya ɗebo Cous-cous da kifi bakinsa yace. “Yah Abanaaa”. Ya ida maganar cikin tsananin so da shaƙuwa. Murmushi Malam yayi kana yace. “Ya dai Babana mai ka samu kake ci haka?”. Murmushi yayi tare da kallon Ishmah yace. “Ina cin girkin Ishmah ne fa Yah Abana”. Kai malam ya jinjina tare da faɗin. “Masha Allah aci abinci sannan ka kula da kanka kaji?”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Toh Yah Abana”. Daga nan sukayi sallama ya kira Addawa ya bata Addawa na amsawa tace. “Ishmah”. Lumshe ido Ishmah tayi cike da son Addawa da kuma rigimarta tace. “Na'am Addawa”. Cike da mutumtaka suka gaisa kana tayi mata ta'aziyya sukayi sallama. Taj kuwa abinci ya cigaba daci bayan ya gama sukayi hira har kusan Azahar kafin ta fita. Washe gari ranan Alhamis akayi sadakan bakwai kasancewar ana amfani ne da yini na rasuwar yasa akayi sadakan a yau ɗin. Da daddare zaune suke a falon Daddy Taj ya kalli Ishmah tare da cewa. “In sha Allahu gobe zan wuce Maiduguri”. Idanunta ta lumshe kana ta buɗe su tace. “Maiduguri fa?,nina ma manta fa Taj”. Kai ya gyaɗa tare da faɗin. “Eh akwai jirgin da zai tashi daga Yola zai wuce Maiduguri ya ɗauki Passingers ɗin Abuja, a Maiduguri kafin su Wuce Abuja so Ni kuma zan bi wannan sai in sauƙa a Maiduguri ”. Cikin gamsuwa tace. “Allah Ubangiji ya kai ka lafiya ya dawo da kai lafiya amma ai baza ka daɗe ba?”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Eh in Sha Allahu in na daɗe ɗin ne inyi kwana huɗu in dawo”. Da sauri tace. “Har kwana huɗu?”. Yana kallon Rahma dake ajiye masu womers a gansu yace. “To ai tagiyarce da yawa daga Birnon zan wuce Zamfara, sai in dawo Kano daga Kano kuma zamu wuce Bauchi daga can sai mu koma Abuja muyi zaman, muna gama zaman kuma zan dawo nan, kafin mu wuce”. Sai muka ya kalli Laylah da Minat dake shigowa yace.... *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 08069423567 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, NA *GARKUWAR MARUBUTA* [1/10, 3:23 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 10* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *LITTAFIN INDA RAI NA KUƊINE, 1k ne cal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853278, ku kuma mutane Niger 1000fc jaka ɗaya kenan rak zaku biya ta wurin Mommy +22790899076, ku biya mu tafi tare domin mun kusa gama free pages* Tsaya-tsaya fa kiji yar uwa. Zuwa yanzu na gama nazari da fahimtar ƙorafe-ƙorafen wasu daga cikinmu mata da kan zomin da kukansu ire-iren haka👉. Garkuwa mijina baida kuzari! Garkuwa mijina yana fin sati biyu ko uku bai buƙaceni ba!. Garkuwa mijina baya gamsar dani in an fara 2 minute yakeyi. A'a Garkuwa wlh abin oga yana ƙanƙancewa. To ku taho ku kuma yi shiru. In sha Allah, da yardar Allah da kuma izininsa da faɗinsa bai sauƙi ko wanne ciwoba Saida ya sauƙi maganin cutar, sai dai in ba'a ganoshi ba. Yar uwa kizo da yaƙini da yarda in Sha Allahu kukanki ya ƙare. Domin akwai haɗin maganin maza. Na basir da sanyi. Domin mafi akasari matsala biyun nanne ke sasu wannan matsalar. Bayan maganin matsalar kuma, akwai zazzafan haɗin maza. Mai magance matsalar ƙanƙancewar gaba, mai ƙara masa kuzari, da girma, gami da iya juriyar daɗewa lokacin raya sunna, da samawa iyali gamsuwar da zata ƙara zaman lfy da inganta farin cikin dararen ma'aurata. Akwai maganin na gargajiya da kuma na Bappa Nasara... “Laylah najin daɗin garin nan fa, ita cewa ma tayi wai in koma in bar mata ke”. Murmushin tayi tare da ruggume Laylah data faɗa jinkinta. Cikin sanyi ta ɗan lumshe Idanunta tare da cewa. “Toh Allah ya kaika lfy y dawo da kai lfy ni ina nan tare da Laylah na”. Ameen ya amsa. Yana mai kallon Minat da saboda kamar ta da Ishmah yasa yake jinta har ransa. Washe gari da Asbah can cikin bacci Ishmah ta fara jiyo sanyayyan sautin muryan sa na ratsa dodon kunnenta daga Masallacin ƙofar gidansu yana karanta Suratul Juma'a. Cikin sauri ta buɗe idanunta tare da miƙewa zaune sai yanzu ta tuna ashe fa yau juma'a ce jin yana karanta suratul juma'a miƙewa tayi tare da tashin Laylah da Minat, kana taje tayi alwala, suma sukayi. Bayan sun idar da sallah sukayi Azkhar sai kuma ta kalli Laylah dake gaisheta amsawa tayi kana ta riƙe hannunta. Yayinda hannunta ɗaya kuma ta shafa kan Minat tare da amsa gaisuwar ta, daga nan suka fito falo hannunta na dama na riƙe da Carbi tana Istigfari... Acan gefen Taj tare da Abba da Yah Muhammad suka fito daga Masallaci suka nufi gefen Abba da kullum suke zuwa shan tea cikin nutsuwa Abba ya kallesa kana yace. “Muje mu duba mutuniyar taka dan jiya da daddare tana ta rakin cewa hannunta ya ƙone”. Da damuwa Taj yace. “Subhanallah amma da dare sosai ko?”. Kai Abba ya gyaɗa suna cigaba da tafiya yace. “Eh kusan ƙarfe goma sha ɗaya Naji tanata raki anzo wajena karɓan Zam-zam ta ƙone kasan Ishmah da raki sai da naje nayi mata tofi kafin ta samu bacci, yanzu ma muje nayi mata”. Ɗan murmushi yayi tare da cewa. “Toh Abba”. Kana sukayi gaba su Yah Muhammad na biye dasu bakinsu ɗauke da sallama suka shiga falon zaune a tsakiyar Parlour suka samesu... Kamar yanda Abba ya sani tana riƙe da hannun tana hura masa iskar bakinta kana tana ɗan yarfewa. Anutse ta ɗago kanta tare da amsa sallamar sai kuma tace. “Yawwa Abba ayi min tofi hannun raɗaɗi yake min ya hanani bacci”. Sai kuma ta maida kallonta kan Khadijah dake cewa. “Ummm”. Ashagwaɓe tace. “Toh me zakice wani ce Ummm?. Keda kike ta baccin ki baki sani ba ya hanani bacci da kyar na samu nayi bacci”. Murmushi Abba yayi cike da kulawa yace. “Shiyasa ma naxo na Miki Tofi Mamana”. Ya ƙare maganar tare da zama kan kushin kasancewar tana kasa ya kamo hannunta yana mata Tofi su Yah Muhammad sai dariya suke suna faɗin rakinta yayi yawa Taj kuwa kallonta yake cike da tausayi da kuma yanda take shagwaɓe fuska kallonsa tayi sai ta sake kwaɓe fuska shima fuska ya kwaɓe kana ya ɗaga mata girarsa ɗaya. Abba kuwa bayan ya gama yace. “Toh ki matso mana Taj ma ya Miki addu'a kinsan kowa da dafa'in bakinsa”. Juyawa tayi ta kallesa sai kuma ta miƙa masa hannu ya mata tofi tare da cewa. “Toh Allah ya sawwaƙa”. “Ameen”. Ta amsa tare da gaishe da Abba kana ta gaishe da Yayunta da Taj. Har zasu fita tace. “Abba in zo musha shayin tare”. Kai ya gyaɗa tare da faɗin. “Zo mana Mamana”. Mikewa tayi tabi bayansu Atare suka sha shayin da ita. Ƙarfe sha ɗaya dai-dai Jirginsu ya tashi daga Yola zuwa Maiduguri borno birnin kanuri bayinmu Fulani. *Sirati sirta moɗa, toh saldori tagga moɗa* kasancewarsu bayi ne a garemu yasa suka koyi karamci da martaba bako, Borno gidan karamci da girmama baƙi tarba na musamman Taj ya samu daga Manyan Malamai Tabbas yaga karamci awajen Kanurai A jiddari aka sauƙe sa bayan ya huta yayi wanka yaci abinci kana akayi masa jagoranci zuwa babban Masallacin Jumma'a Al-Ansar. Kusan a tare suka shiga yana tsakiyar Al Sheiky Zharma.. Imam Muchmah. Da kuma Al Sheiky Idee sun sashi a tsakiya yayinda. Dubban musulmai ke dandazon shiga ciki masallacin shi yayi musu limancin Sallar juma'a na wannan ranan. Koda aka idar tuni matasan Borno suka zagayeshi nan sukayi ta gaisawa dashi tare da yin hotuna da vidios suna yaɗawa a social media, tuni Nigeria ta ɗauka cewa Sheykh Afif Muhammad Taj na cikin ƙasar. Washe gari Asabar bayan an idar da sallan asuba ya wuce garin Zamfara, nan ma yaga karamci. Kamar yadda ya alƙawaranta haka ya limamcesu kamsusul salawat. Daga Zamfara ya wuce Kano ta dabo tumbin Giwa. Jallabar hausa. Ya Salam shine abun da yake faɗa a lokacin da ya dira a malam Aminu Kano international airport, sabida ganin taron masoya mabiya karatuttukan. Bisa jagorancin Malam Aminu Ibraahim Daurawa da tsaron hukumar Hisba suka tarbeshi har zuwa masauƙinsa na musamman da aka tanadar. Taj yaga karamci iya ka wurin kanawa. Dole kwanan sa biyu a Kano. Ishmah ce zaune bisa kujera riƙe da cup ɗin da da Khadijah ta dama furar mata ta kasa sha, ɗan kwafe fuska tayi lokacin da ta kurbi damun, domin ba daɗi kam to Amman akan ya lalace ai gwara ta shanye musamman in ta tuna gargaɗin Garkuwa gyara riƙon da tayiwa wayarta tayi tare da cewa. “Yanzu dai ai yau zaku wuce Bauchi ko”. Yana mai ɗan sunkuyar da kansa kasancewar wayar na aljihunsa ne domin rashin samun lokacin kansa yace. “Eh yanzuma zamu tafi”. Cikin kula tace. “Taj anya kuwa kana cin abinci yadda ya kamata Allah naga videos ɗinka ka ɗan rame, gashi kanawa nan yan al'barka sun zagaye min kai yadda kake ta musabaha da mutane a gajiye”. Yana ɗan lumshe idanunsa dake cike da tarin gajiya yace. “Suna da karamci Amman yawan su da yawan son da suke min yasa sun kasa barina in huta”. Cikin sanyi tace. “Bari in Barka dan naji yanzuma cikin mutane kake”. Cikin sanyi yace. “In sha Allah jibi zan dawo dan yau in munje Bauchi da dare zamubi jirgi zuwa Abuja. Duk zaman da zamuyi gobe zamu gama a Abuja jibi da sassafe zan iso Yola”. “Toh Allah ya kawoka lfy Amman Please ka kularwa Meymey da kanka da Adaya”. Da sauri ya rumtse idanunsa tare da katse kiransa saboda tsinkewa da zuciyarsa keyi a duk sanda ta kira mishi su more especially Adaya. A ranar suka wuce Bauchi. Sha biyu dai-dai suka isa Bauchi Yakubu. Kai tsaye suka wuce gidan, Sheykh Tajuh Usman Bauchi, dottijon malami kuma sannane a cikin ƙasar mu da kewaye baki ɗaya, Shekh Tajuh Usman Bauchi dottijon mai tarin limin addini da yawan shekaru kana da zugar zuriya ƴaƴa da jikoki da jikokin jikoki, malami ne na Ɗarika tsakakkeyiyar ɗarika. Wanda yake da good understanding da manyan malaman kasarmu na sunan, shiyasa tafiyar ma dasu akayi suna shiga harabar gidan Taj ya lumsh idanunsa tare da sauƙe wani irin amintaccen ajiyan zuciya da fesar da sassayan numfashi kana ya buɗe idanun a hankali yana karewa tsarin gidan da yafi dacewa da a kira shi da fada ko masararuta ilimi isilam domin girmanshi ya wuce ace dashi gida, tsaruwarsa kuwa yafi karfin ace dashi ko sangaya sai dai masarautar. Isarsu ba wuya akayi musu iso cikin asalin sashin Sheykh Tajuh Usman Bauchi. Kusan a jere a jere suke tafiya cike da kamala da nitsuwa da ilimi addinin Musulunci ya sakar musu, yayinda yan agajin da kuma jami'an hukumar Hisba ke zagaye dasu. Kusan duk a tare suke sauƙe sassauke numfashi a hankali da tsuka ratsa tsakiyar wani mashahurin Parlour na alfarmar. Sai kuma duk suka ɗan tsaya saboda, ganin ɗaya daga cikin masu yi musu jagoran ya ɗan buɗe musu wata babbar ƙofa tare dacewa Bismillah. Manyan malaman sunan a gaba, yayinda suka sa Taj a tsakiya sai yan agajin dake baya, kusan duk a tare sukayi sallama Ya Salam. Shine abinda Taj ya faɗa a lokacin da suka iso tsakiyar Parlour da yafi dacewa da a kira shi da holl, sai kuma ya lumshe idanunsa saboda hango Sheykh Tajuh Usman Bauchi dake zaune a tsakiyar ƴaƴansa da jikokinsa gami da kuma amintattun ɗalibansa duk sun zagayeshi tamkar sarki a tsakiyar waziransa. Haka nan sai yanayin yayi mishi kama da yadda suke sa Yah Abana a tsakiyar duk ranar jumma'ar ƙarshen ko wanne wata, komai na zaman da tsarin gidan yayi mishi tuni da gidansu. A hankali ya buɗe idanunsa tare da diresu kan kekkyawan farin dottijon. Kusan a tare shi da Dottijon suke rufe idanunsu Saboda wani irin fitinenne bugun zuciyarsu da yayi a tare. Yayinda sauran kuwa duk sun zube a tsakiyar Parlour a gaban dottijon da duk ya girme su, yana haifesu wasuma yayi jika dasu. Yayinda sauran yaransa kuwa duk suka juyo suna kallon inda mahaifin nasu ke kallo. Malaman Sunnan kuwa da sukazo cike da girmamawa suke gaida Sheykh Tajuh Usman Bauchi. Amman ina hankalinsa baya kansu. Ido ya zuba wa Taj tamkar zai mannesu a jikinsa. Shi ma Taj idon ya zuba mishi yana mai ɗan matsowa kusa da abokan tafiyar tasa. Sai kuma duk taron jama'ar da suka samu a Parlour suka juyo da sauri suka zubawa Dottijon idanu jin yana mgna cikin muryar girma da nitsuwa da tsufa mai nagarta yace. “Inajin Ƙamshin Mahmoudu na, ƙamshin Mahmoudu nakeji”. Ya ƙare maganar da miƙawa Taj hannunsa tare da cewa. “Afif Muhammad Taj ne yau a sangayata”. Da sauri Taj ya miƙa masa hannunsa. Jawosa kusa dashi, Da sauri Taj ɗin ya ɗan rusuna tare da direwa bisa guiwowinshi, Shi kuwa Sheykh Tajuh Usman Bauchi, kan Taj ɗin ya ɗaura bisa cinyarsa, sai kuma ya sunkuyi tare da cusa hancinsa cikin sumar kan Taj, tare da shaƙar ƙamshin jikinsa. Numfashi mai sanyi ya fesar tare da ɗago kanshi ya kalli baƙin nasa tare da cewa. “Izala ƙanwar ɗarika yau kun kawo min baƙo na musamman, bakon da nake jin jini da zuciyata sun aminta dashi”. Sheikh Jabeer sani Maihula ne yayi ɗan murmushi cikin sokkotancinsa yace. “Malam ai ayanzu Sunnan ce abbabba ɗarika ce aƙƙarama, kawai kui mubaya'a ku yarda mune ag gaba gareku”. Murmushin Dottijon yayi tare da cewa. “Yoh aiko ɗan hodiya mancewa yayi a sauka Sokoto da Bauchi zaizo”. Dariya sukayi mai sauti sai kuma duk suka fara gaisawa, har lau dai Sheykh Tajuh Usman Bauchi bai saki Taj ba, yayinda ƴaƴan da jikokinsa kuwa kab idonsu na kan Taj. “To Alhamdulillah sannu ku da isa lfy”. Sai kuma ya ɗan kalli gefen damansa tare da cewa. “Ku isa kusha ruwa kuzo muyi muƙabala”. Da sauri Sheykh Daurawa yace. “A'a Malam zafa kayi mubaya'ar nan da baka sonyi in mukayi muƙabala”. Sai kuma suka kalli Sheykh Janeer dake cewa “Awoh haɗimai Gsky dai, domin hujjar aggaremu gaba gareku, kuna gani da ajjiyarku zaku dawo baya garemu, ko ku zam kuna ɗumi”. Dariya sosai sukeyi musamman sokotancin da Sheykh Jabeer ke zubawa. A hankali ya yunƙura tare da fara kiciniyar miƙewa, da sauri Taj ya tallabeshi tare da taimaka mishi ya miƙe, sai kuma yayi saurin amsar sandar da mutumin dake gefensa ya miƙa mishi. Amsa yayi tare da bawa dottijon shi kuwa Sheykh Tajuh Usman Bauchi cikin tarin girma da isar kamala yace. “Ni bana gaisawa da baƙo har sai na bashi abin sha da ci yaci ya sha, dan haka Bismillah ku iso nan ya ƙare maganar yana nuna musu Dinnin area. Wani tamfatsetsen Dinnin table ne na alfarmar wanda ke da kujeru goma sha huɗu. Yayinda saman table ɗin ke cike maƙil da kayan marmari da kuma manyan womers na alfarmar sai plates, bowls, mugs, and spoons. Sanin YESS bazai tsaya yayi mgn ba sai sun sha wani abune yasa suka nufi Dinnin area ɗin bisa jagorancin babban ɗansa. Sheykh Tijjani. Ga mamankisu kuwa sai gani sukayi yaja hannun Taj. Sun bi wata ƙofa ta musamman sun tafi. Kusan duk yayansa kallon kallo suka farayiwa juna, fuskokinsu ɗauke da maɗaukakin mamaki. Su Sheykh Jabeer kuwa. Bayan sun ci sun shane, duk sukayi al'wala saboda jin an kira salla. Daga nan suka wuce masallacin sangayar. Murmushin Daurawa yayi lokacin da suke tsaye a sahun forko sai kuma ya kalli Sheykh Musa Yusuf Asadussunah na faɗin. “Toh yau maji ma gani wa zai limamce, izala zata limancin ɗarika ko ɗarikace zata limancin izala”. Murmushin Sheykh Isa Ali Pantami yayi tare da cewa. “Mu mun basu dama”. Da sauri Sheykh Janeer yace. “Anya ko munefa gaba garesu”. Murmushin Sheykh Tijjani yayi yana kallon mahaifinsa ganin yana jawo hannun Sheykh Afif Muhammad Taj. Ga mamakin duk al'ummar Annabi dake cikin yankin jin Dottijon yana faɗin. “Yau ba ni zan ja sallaba ya faɗa tare da ɗan matsawa gefe kana yaci ga da cewa. “Alhamdulillah dai ga Afif Muhammad Taj, a ƙasar Nigeria a kuma jahar Bauchi a tsakiyar tsagayata a kuma sahun limamcin masallancimu.” Ya ƙare maganar yana jawo hannun Taj ya tsaida shi da'irar limancin kana ya koma ya tsaya a sahun forko. Shi kuwa Taj zuwa yanzu al'amarin dottijon ya daina bashi mmki kawai dai yana jinsa har cikin jini da tsoka ƙashi da bargo jiki da zuciyarsa, wani irin son dottijon yakeji yana game jiki da zuciyarsa. Cikin sanyi ya gyara tsayuwarsa tare da gyara maek ɗin cikin nitsuwa gami da cikir kamala ya ɗanyi gyaran murya tare da cewa. “Sahoohhhh! Sahoooohhh!! Sahooooooohhhhh!!!”. Kusan gaba ɗaya mamun nasa lullumshe idanu sukayi saboda yadda sautin Muryasa yake ratsadu, sai kuma duk suka gyaggyara tsayuwar sahun. Ajiyoyin zuciya suka rinƙa sauƙewa tare da bubbuɗe kwayar idanunsa lokacin daya fara tada iƙama. Da yawa sunso ace jam'in sallama Magrib ko Isha ko asuba zai jasu dan suji zaƙin muryasar. Bayan an idar da salla suna sake koma ciki. Nan suka tattauna duk abinda ya kawosu. Kasan cewar Sheykh Afif Muhammad Taj da Isa Ali Pantami da Sheykh Jabeer Sani Maihula da wasunsu Abuja zasu wuce, kuma sai tara na dare jirginsu zai tashi ne yasa suka kai dare. Saura kuma tun bayan la'asar suka juya suka koma Kano. Sit kakaji masallacin da lokacin da yake jansu sallan Magrib babu abinda ke tashi sai sautin muryarsa bayan ya karanta suratul Fatiha kana ya ɗaura. Daga forkon Suratul Yoosuf “(Aliflamrah tilka ayatu alkitabi almubinu)”. Daga nan yaci gaba da kawo ayoyin har yaje aya ta 10 kana sukayi sujjadar forko, kana suka miƙe dan. Cikin aminci ya karanta suratul Fatiha kana ɗaura da Suratul Yusuf ɗin ya ɗauka daga aya ta 11. (Qaloo ya Abana ma laka la tamanna Aaala Yoosufa wainna lahu lanasihoona”.) Wasu irin tafassasun hawayene suka zubawa Sheykh Tajuh Usman Bauchi, Dottijon mai cike da wani miki a zuciya, yayinda shi kuwa Taj haka nan yaji tsoro na diro mishi cikin danne rauninsa ya kawo aya ta 12. “( Arsilhu ma'AAana ghadan yartaAA wayalAAab wainna lahu lahafithoona”. Numfashi mai nauyi ya fesar a hankali tare da baddashi cikin taƙib kana yaci gaba da kawo ayoyin Saida yaje aya ta 20. Kana suka tafi ruku. Haka dai sukayi sallan cike nitsuwa da amcin mu'ujizar Alqur'ani mai girma. Koda suka idar basu fitaba sai da sukayi isha, anan ma duk a Suratul Yusuf ya jasu, wanda duk aya goma goma ya rinƙa kawowa haka yasa aka samu ayoyi 40 kenan Ƙarfe tara dai-dai jirginsu ya tashi zuwa Abuja. Cikin alfarmar darajar Alqur'ani mai girma. Aka ɗaukesu kai tsaye gidan Sheykh Isa Ali Pantami suka wuce. Taj yaga kara da mutumci iyaka a wurin wannan Bagombe ya nuna mishi kuma lallay Gombawa ɗiban farine, ba'a kwana dasu ba a tashi dasu. A dare ranar yaga karrama. Washe gari da safe, cikin mutuntawa Sheykh Isa Ali Pantami ya shiga masauƙin baƙon nasa. Shi kuwa Taj a dai-dai lokacin waya yakeyi da Ummeey ya kuma haɗa comfrence call ne da Ishmah sai dai Ummeeyshi bata saniba. “Babana wai sai yaushe zaka dawo ne? Ko ka mance cewa ka tafi ka bar mararka ne, yau fa sai nan tazo muka kwana, tace gaba ɗaya ƙasar Ethiopia batayi mata daɗi in baka nan”. Sai kuma ta ɗanyi shiru. Shi kuwa Taj a hankali ya gyara tsayuwarsa tare da ɗan gyara zaman hular kansa yana mai nazari kan wasu ababen sauye-sauyen Meymey da sam a zuciyarsa bai aminta da itaba. “Hello Babana kayi shiru, ɗazu munyi waya da Laylah tace wai bakusa ranaba me haka ke nufi?”. Cikin sanyi murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Yanzu ina Abuja gobe Thursday zan koma Yola. In sha Allah ranar Sunday zan iso Ethiopia domin in samu in ɗan huta dan inada tafiya ranar Tuesday, kuma Ummeey malam ƙasar ne suka ɗan riƙeni shiyasa.” Ya ƙare maganar cikin Yaren Amharic wanda shine asalin Yaren Ummeeyshi, yayi mgnar cikin sanyi tare da juyowa jin sallar Sheykh Isa Ali Pantami. Da sauri ya sallami Ummynsh tare da katse wayar. Ruggume juna sukayi shida Sheykh Isa Ali Pantami. Yayinda PA'nsa keta ɗaukarsu hoto, gami da ɗan video. Bayan sun gaisa ne suka wuce wurin taronsu da manyan malam Sunnan. Inda suka bashi kyautar murya kira'a mafi daɗi da soyuwa a shekarar. Washe gari da safe jirginsu ya tashi daga Abuja zuwa Adamawa Yola Cikin farin ciki da jin daɗin mutumtaka da kima daya samu daga Manyan Malamai da kuma jama'ar Nigeria. Yah Abubakar ne ya ɗaukoshi a Airport ɗin. Awaje suka haɗu da Abba wanda ya fito daga Masallaci bisa alamu yayi walaha ne. Cikin so da kulawa Abba ya ɗan ruggumeshi tare da cewa. “Barka da sauƙa lfy”. Sai kuma ya kalli Adam daya buɗe but ɗin motar ya fito da jakarsa yana ɗan ja. “Masha Allah isa daga ciki, ka samu ka huta, kasha zirga-zirga a titunan ƙasarmun nan da ba cikekken kyaune da suba bare tsaro”. Kai ya ɗan jinjina domin Allah ya sani a gajiye yake, ga yunwa dake kwaƙular cikinsa haka Allah yayinsa baya iya cin abincin kirki in ba matsa mishi akayi ba, so yake yayi wanka yaci abinci yayi bacci. Shi yasa yana shiga BQ ɗin kai tsaye bedroom ya wuce. Adam kuma jakar tasa ya ajiye mishi kana ya nufi cikin gida. A kitchen ya samu Ishmah tsaye cikin wani tattausan lace pink and sky blue collar mai ɗan ratsin Royal blue. Ɗinkin doguwar rigace da Idris ɗinta ya watsa mishi ɗinki na alfarmar, sosai ya zauna a jinkinta ɗas da ita. Sai wani irin fitinenne ƙamshi take zubawa, ta murza daurin a setta tayi kyau sosai a ciki. A hankali take motsa gas meat and Emargency Sultan chips da yaji naman kaza ziryan ɗinta ba ƙashi ko kaɗan sai ɗan Vegetables kaɗan. lashe baki yayi tare da cewa. “Uncle Taj ya iso fa”. Da sauri ta juyo dan bata san ya shigo ba. “Ya Salam to miƙo min Food flack' and mug ɗinnan”. Ta ƙare maganar tana jawo trayn. Miƙo mata yayi tare da ɗan jawo plate ya miƙa mata kana yace. “Toh nima a saka min a nan”. Tana juye Gas meat ɗin a wani kekkyawan food flack's dan madaidacin tace to. Sai kuma ta juyo Sultan chips ɗin ma. Kana duk ta jerasu a kan tray ɗin. Sai kuma tasa plate, bowl, mug, sai spoon and fork. Duk ta jerasu kana ta miƙa mishi tray tare da cewa. “Yauwa gashi ka kai kan Dinnin table na BQ sai ka dawo ka amshi naka. Sannan ka ɗauko min Laylah a gidansu Minat, tun juya suka tafi basu dawoba gashi ya dawo bata nan”. To kawai yace kana ya ɗauki trayn ya juya ya fita dan sauri yake ya samu ya dawo yaci wannan haɗin. Ita kuwa Ishmah da sauri ta buɗe fridge Yoghurt fruits data haɗa mishi ta ɗauka tare da faro water ta sasu a tray tare da glass cup. Kana ta fito, a Falo ta samu Rahman bisa alamu da Khadijah take waya dan jin tana cewa. “Tunda kika komafa nake ta cewa ki haɗani da Maamah amman kinƙi, Maamah ɗiyar Khadijah babbar kenan”. Tana fita ne tace mata. “Please ki gyara kitchen nan, kuma ki maida tukunyar danderun nan kan gas”. Tana miƙewa tsaye tace to. Shi kuwa Taj a hankali yake feshe jikinsa da turare, lokacin da ya gama kimtsa kansa cikin tattausar jallabiyarsa Black collor. Ɗan gajere tsaki yaja tare da gyara robar boxer ɗin jikinsa. Allah ya sani shi baya son takura, musamman ma Taj ɗinsa dake fama da tsaurin ido, shiyasa in a gidansa yake baya iya zama da Boxers dan bazai iya takura kansaba Allah bai takurashi ba. A hankali ya ɗan shafa cikinsa jin yadda ya ɗanyu ƙugin yunwa. A hankali ya fito Parlour. Dai-dai lokacin kuma Ishmah ke ajiye trayn hannunta bisa Dinnin table ɗin kana ta kalli Khairat ɗiyar Yah Abubakar wacce saboda Laylah bata nanne yasa ta biya ta ɗaukota suka taho tare. A tare suka sauƙe numfashi mai nauyi kamar da sauri ya kuma rumtsa idanunsa saboda jin alamun zaiyi loosing confidence ɗinsa aiko tuni ya gaza control ɗin bakinsa kamar a fizge yaji yace. “I miss you so much Ishmah”. Wani tattausan murmushi ta sakar mushi tare cewa. “Miss U to my friend”. Ɗan kwaɓe fuska yayi tare da shafa kan Khairat kana ya ɗan kalli bayan Ishmah yace. “Laylah fa?”. Kujerar dinnin table ɗin ta jawo mishi tare da cewa. “Bismillah zauna, Laylah tana gidansu Minat yanzu Adam zai ɗaukota”. Cikin sauƙe numfashi gaji ya zauna tare da juya gajiyayyun idanunsa murya a gajiye yace. “Im tired my heart”. Ya ƙarashe mgnar can ƙasan maƙoshinsa saboda shi kansa baisan ta fitoba, hakazalika itama bataji ƙarshenba. Cikin tausayawa da kulawa tace. “So sorry sun gajiyar da mijin Meymey ko”. Ganin kallon da yayi mata ne yasa tayi saurin yin ƙasa da kanta, kana a hankali ya jawo trayn nan Yoghurt fruit ɗin ta zuba mishi a bowl mai ɗan girma kana tasa mishi table spoon tare da miƙa mishi tana faɗin. “Gashi fara da wannan kafin in zuba maka abinci, so nake ka shanye kafin in zuba maka”. Amsa yayi tare da ɗan lumshe idanunsa su huɗune kacal suke mishi haka a duniya. Ummeeyshi, Yah Abana, Addawa, da kuma ita, sai kuma Aunty Rashidansa. Ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙe lokacin da ya kai Yoghurt fruit ɗin bakinsa ya Salam, garɗin madara Apple Banana da kuma zaƙin inabi ne suka haɗu suka sashi fara sha. Murmushi tayi tare da kallon Khairat dake cewa. “Goggo Ishmah bani wayarki”. Miƙa mata wayar tayi kana ta ɗauki plate gefe kaɗan ta sa mishi farar shinkafa, tare da ɗan ɗaura yankakken lemun tsami daya a kai, sai kuma gefen tasa Sultan chips ɗin ɗaya gefen kuma tasa gas meat ɗin da yake zuba ƙamshin da kan iya tada yunwa. Cikin kulawa ta ɗan jawo bowl ɗin gabanshi ganin ya shanye saura kaɗan, Table spoon da fork ta sa mishi a gefe da gefen, kana ta miƙa mishi. Da sauri ya fidda idanunsa waje alamun yayi yawa. Ita kuwa kwaɓe fuska tayi cikin yanayin da bata san tana shigaba tace. “Please ka cinye”. Ta ƙare maganar tana sa mishi ruwa a glass cup ɗin. Shi kuwa Taj kanshi ya ɗan longwaɓar yana yi mata wani irin amintaccen kallon dake fita daga wani sirri daga can cikin ƙahon zuciyarsa yana cusa shi cikin tata zuciyar a sirrance. Ganin ta tura bakine yasa ya fara ci. Ya salam ya gamsu Ishmah ƙarshece a komai. Yanayin yadda ta haɗa mishi abincin kawai ya ishe ka sha'awa. A hankali ya fara ci suna ɗan hira. “Uhmmm kasan yanzu naga an buɗe TikTok da IG da sunanka sosai, har Channel aka buɗe a You tube da sunanka. Suna ta saka karatuttukanka.” Murmushin yayi tare da tauna tsokar kazan da yasa a baki yace. “Da haka suma zasu samu lada”. Ruwan ta miƙa mishi tare da cewa. “Harma da kuɗi ai ƴan You tube kam zasu samu”. Kanshi ya jinjina tare da zuba mata ido jin tace. “Wannan trolling fa, naga bada shi ka tafi ba”. Ruwan ya ɗan kurɓa tare da cewa. “Gomnan Borno ne zulum yayi min irin kyautar da kikayi min, da naje Bauchi kuma Sheykh Tajuh Usman Bauchi shima ya bani tsala-tsalan alƙyabbu guda uku, harda rawaninsa”. Cikin murmushi tace. “Basu dai haɗa maka da mata ba kam ko? Dan naga yadda suke ta ribibinka nace wannan dai da alama zasu baka mata biyu ka cika ta huɗunka a Nigeria”. A hankali ya ture plate ɗin tare da jawo Tissue box. Ita kuwa plate ɗin ta kalla yaci yafi rabi, tunda yazo ma baici abinci mai yawa kamar hakaba, hakanne yasa ta ɗauki ɗaya plate ɗin ta rufe abincin kana ta tura trayns ɗin gefe. Shi kuwa Taj ruwa yasha, sassayan gyatsa yayi tare da cewa. “Alhamdulillah”. Ita kuwa Ishmah a hankali tace. “Ɓoye min zakayi dan an baka mata a ƙasarm..” Sai kuma tayi shiru tare da ɗan zuba mishi idanunta saboda ganin yadda ya longwaɓar da kansa kana idanunsa sukayi jazir, lip inshi na ƙasa ya ɗan ciza murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Ai dama kafin in samu matar aure a ko ina a faɗin duniya a Nigeria na fara samu, damace da ban samuba, da ƙaddara dake ta ɗawainiya da rayuwata yasa bamu kasance a tare a inuwar aureba”. Da sauri tace. “Taj a Nigeria kuma? Wacece ita? Me sunanta? Yaushe kuka haɗu? Meyasa baka gaya min ba?”. Kafe kwayar idanunsa yayi cikin nata, itanma shi ta tsare da idanunta tana jiran amsarta cikin sanyi ya motsa lips inshi a hankali yace. “Ita na fara sani kafin ko wacce mace, bayan Mahaifiyata kakata da yayuna mata. Rashin ta ne yasa ƙaddara samun damar juya rayuwata, domin da na aureta bazan taɓa auren wata ɗiya mace ba a duniya, ita kaɗai ta isheni, inada yaƙini zata kula dani kulawar da mata huɗu zasuyi min, shiyasa a kanta na ajiye burina na auren mata huɗu, domin da wannan burin na tashi a rayuwata Inyi mata huɗu kamar Yah Abana, ko wacce ta haifa min yaya 12 ko 6-6 Kinga in na samu ƴaƴan sha bibbiya zan samu yaya 48 in kuma shida shida na samu kinga 24, Inyi musu irin tarbiyyar da Yah Abana yayi mana, domin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallam yayi alfahari dasu a ranar goɓe ƙiyama.” Sai kuma ya fesar da wani irin raunataccen numfashi mai cike da dafin so kana ya juya gajiyayyun idanunsa cikin nata. Hakan yasata kasa janye idonta cikin nata. Shi kuwa Taj murya can ƙasan maƙoshinsa yaci gaba da cewa. “Tun randa na ganta naji na janye wannan burin domin nasan zatayi min duk abinda mata huɗu zasumin, kuma bazan iya yi mata kishiyaba dan inayi mata kishin kaina da kaina, dan nasan in na aureta ta isheni ko yaya 6 ko biyu ta haifa min sun isheni kai ko bata haihuba zan rayu da ita, kin mance ina gaya miki in na auri wacce rai da zuciyata keso bazan mata kishiya ba”. Ya ƙare maganar da iyakar gsky zuciyarsa, da sauri tace. “Taj ashe akwai wani abu naka a duniya da kake ɓoye min ban saniba, toma me yasa baka aureta ba Taj?”. Cikin sanyin halinsa da murya yace. “Ɓoyeyyiyar ƙaddara, bata buƙatar namiji irina, gashi kuma Kinga yadda ƙaddara ta kawo Meymey cikin rayuwata, ke kuma kika liƙo min Adaya a rayuwata, so yanzu bani ba ƙara aure a duniya, domin zan bar gurbin wacce nakeso, shiyasa bazan taɓa cika mata huɗuba, dole zan bar gurbin da duk randa ta soni so na aure zan aureta”. Ido kawai ta zura mishi tana mamakin kalamansa. Sai kuma tayi saurin cewa. “Yauwa ya batun Adaya ma yaushe zata tare”. Da sauri yace. “Kiyiwa Allah ki bar brain ɗina ya huta”. Ya ƙarashe maganar cike da alamun tarin bacci da gajiya. Da sauri tace. “Toh amman wai meyasa baka haɗani da Meymey ba, ko ta'aziya baka bari tayi min ba”. Yana miƙewa tsaye yace. “Nace miki bazan taɓa haɗaki da duk wacce akace matata bace”. Da sauri tace. “Wai dan Allah saboda menene?”. Ba tare daya bari ta ƙarasa mgnar ba yace. “Saboda kada wata rana suce, kin munafurcesu ko kin hancincesu koma suce kinci amanarsu”. Da sauri itama ta miƙe tsaye. Sai kuma ta tsaya ganin ya juyo ya zuba mata ido tare da cewa. “Itama dayar shiyasa ban haɗaku ba”. Ta buɗi baki zatayi mgna kenan akayi kiran salla. Haka yasa tayi shiru. Bayan sun gama bin kiran sallan da yin addu'a ne ya ɗan kalleta tare da cewa. “Da jarida kika karanta dan shi ya dace dake ba aikin likitanci ba. Kin wani tsareni da tambayoyi tuhuma, takaicina ma ba gane komai zakiyi ba, Ni bari inje inyi salla in na dawo kuma zanyi bacci ne”. Da ido ta rakashi har ya ɓacewa ganinta, daga nan itama ta kama hannun Khairat suka nufi side ɗin Aunty Nana a falonta suka sameta tana salla, itama salla ta niyanta. Azahar yana dawowa yayi baccinsa, kiran salla la'asar ne ya tada shi. Suna dawowa su Laylah na shigowa da gudu suka nufi BQ ɗin ganin ya shiga, Mahmoud, Minat, Khalid, da kuma Khairat cikin nitsuwar tarbiyya suka gaidashi daga nan suka fara kallon Tom and Jerry da akeyi. Shi kuwa Taj System nashi ya ɗauka ya fara duba shirye-shirye tafiyar da zayyi da ƙasashen da zai jajje in ya koma ma sai yayi kusan mako biyu yana zirga-zirga in yayi hutun mako ɗaya kuma zai sake tafiyar da zayyi kwana goma. Yau asabar, ta kama gobe Sunday ne jirgin Adamawa to Abuja zai tashi da safe, na Nigeria to Ethiopia kuma zai tashi da yamma. Bayan an idar da sallan la'asar ɗin. tare suka shiga falon Abba cikin sauƙe numfashi Abba ya kallesa kana yace. “Tajuddeen ɗazu da muke shigowa naji kamar kana cemin yaushe zaka tafi?”. Cikin girmamawa da mutumtaka ya gyaɗa kai tare da cewa. “Eh Abba in Sha Allahu ina so gobe zan tafi Abuja daga nan zan wuce Ethiopia da yamma”. Ajiyar zuciya mai nauyi Abba ya sauke kana cikin fesar da numfashi yace. “Taju mun gode Ubangiji Allah ya saka da al'khairi”. Kansa aƙasa ya amsa da. “Ameen ya Allah Abba”. Numfashi mai nauyi Abba yaja kana ya fesar tare da cewa. “Taju akwai wata alfarma da nake nema awajenka”. Cikin wani irin baƙon yanayin da zuciya ke ɗauka abaxata ya kalli Abba cike da girmamawa yace. “Abba Kace Umarni zaka bani ba alfarma zaka nema ba. Saboda kafi ƙarfin neman alfarma awajena sai dai ka bani Umarni kamar yanda Yah Abana zai bani Umarni”. Zama Abba ya gyara kana ya fuskancesa da kyau cikin gskyar zuciya da amincin da yakeji akan Taj ɗin yace. ”Um-um Tajuddeen Alfarman dai nake nema”. Cikin jin nauyi da ganin kimansa ya sake risinar da kansa tare da cewa. “Abba idan kana faɗin haka kunya nake ji”. Kai Abba ya girgiza cikin sauke ajiyar zuciya da sanin kiman da muntuncin Taj yace. “A'a Tajuddeen dole ne ince haka”. Manyan Idanunsa Masu haske ya lumshe Muryarsa dake cike da nutsuwa ya gyara tare da faɗin. “Abba wace alfarma ce wannan?”. Zama Abba ya gyara kana yace. “Tajudden Nasan al'aƙarka da kai da Mamana alaƙace data kasance mai tsabta cike da tsarkakekke zuƙata, irin hasken nan dake haskaka juna wanda aka gina saboda Allah kasan irin ƙaddarar dake bibbiyar rayuwar Mamana?”. Cikin wani irin yanayi mai gauraye da zaƙuwar jin ƙarshen mgnar ya jinjina kai. Tare da sunkuyar da kansa ƙasa Muryarsa cike da sanyin da ƙasan sa farin cikine yace. “Sosai ma Abba na sani”. Cikin damuwa da rauni Abba yace. “N.....! Littafin nan dai na kuɗine ki biya ki karanta cikin aminci 1k ne 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa. *BY* *GARKUWAR MARUBUTA* [1/13, 1:34 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 11* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin INDA RAI na kiɗine wannan free pages ne mukeyi kuma suna gab da ƙarewa, 1k ne kacal kuɗin samur karanta littafin ki saya ki karanta cikin aminci. 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. Mutanen kasar Niger kuma 1000fc ne jaka ɗaya kenan rak zaku tura Kuɗin karanta littafin +22790899076 ita zakuyiwa magana* “Nasan cewa tana fuskantar matsala akan Aure, amma itama ya kamata ace ta gyara niyarta, banason in matsa mata saboda banason tayi tunanin na takura mata akan matsalar rashin Aure, bana kuma jin daɗin zamanta haka babu aure abin yana min ciwo yana hanani bacci Tajuddeen, domin mutane laifina suke gani, faɗi ake na barta tana abinda takeso ta hau babbar mota taje aiki tana zirya a gari ba aure”. Cikin tausaya Taj yace. “Bakomai Abba in Sha Allahu watarana zai wuce kamar bai faru ba”. Cikin sauƙe ajiyar zuciya Abba ya gyara zamansa tare da cewa. “Haka nake fata shiyasa nake so ka taimaka min da wani abu saboda naga Mamana tana fahimtar maganar ka tana kuma jin shawararka”. Ahankali Taj ya sake sunkuyar da kansa ƙasa yana mai sauraron bugun zuciyarsa dake tabbatar da mgnar Abba haka take, yasan Ishmah na bin shawararsa sosai yasan akwai good understanding a tsakaninsu. Abba kuwa cikin sanyi da yaƙinin Taj zai fahimtar da Ishmah ya cigaba da cewa. “Kaga ga Mahaifin Yaranta nan yana sonta yana ta ziryan zuwa zai maida ita itace taƙi bada haɗin kai, bamu sani ba wala Allah Rabo ta dashi ne yaketa kauda sauran Mutanen da suke zirya wurinta. Zuwa yanzu Yayana Muhammad Bello, ya fusata a kaina, baya ƙasar ne shiyasa baku gabana, ya tafi Uhmra dashi da iyalansa, kuma da yake su a Gombe suke da sauran ƙannena zaman aiki ne ya kaisu can duk mafiya akasarin Family na suna Gombe, babban yayan mu ya fusata sosai a kan Aysha yace min kusan dominta ya tafi umra zai roƙi Allah yayi mata zaɓi da mafi alkhairi, ya tabbatar min wlh muddin ya dawo zai ɗaura mata aure da duk wanda yaga dama ko tana so ko bata so. To dan Allah ka tayani bata baki sannan ka nuna mata amfani da muhimmanci yin auren da kuma muhimmancin komawa kan ƴaƴanta saboda ɗa sai da Uwarsa kuma itama uwa saida ƴaƴanta, ka sanar mata yadda mukayi da ɗan uwana in fa ta sake har ya dawo ya huta gajiya ya taho daga Gombe zuwa nan tofa tayi kuka da kanta a kan duk abinda yayi mata ta sanshi tasan halinshi zai aikata duk abinda yace, gashi suna tare da wasu manemanta a can Gombe”. Lokaci ɗaya yaji zuciyarsa tana bugawa yayinda zufa ya shiga tsatstsafo masa duk da sanyin da ake yi ga kuma sanyin AC. Haka nan yake ji kamar wani abu mai masifar nauyi ne Abba keson ɗaura mishi, ji yake yi kalaman Abba na firgitashi kana suna sauƙa a kan jiki da zuciyarsa tamkar rushi yake watsa mishi, shiru yayi batare da yace komai ba saboda lips inshi sun mishi nauyi... Abba kuwa ganin yanayinsa ne yasashi sauƙe ajiyar zuciya tare da faɗin. “Tajuddeen Shiyasa nace maka al'farma nake nema saboda na san zakayi tunanin idan kasa baki acikin maganar zata yi fushi da kai ko wani abu amma koda tayi fushi da kai nan gaba zata fahimci gaskiya ka faɗa mata tunda dama ai ita gaskiya ɗaya ce daga ƙinta sai ɓata”. Kai Taj ya jinjina ba tare da ya iya motsa lips inshi ba. Abba na gyara zama yace. “Toh ka nuna mata muhimmanci haka idan kuma tace. Dr Nafi'u zata jira toh ta cigaba da jiranshi amma Dr Nafi'u bazai Aureta ba ka gani tun yaushe ake abu daya sai abu yazo sai yaja kwanaki”. Runtse Idanu Taj yayi cikin tsananin bugun zuciya daya baibaye shi. Abba kuwa cigaba da cewa. “Ko yaushe sai jan kwanaki yake yanzu haka ya dawo yace wai akwai wani course da zai je Indi'a yayi na wata shida sai dai ta jira idan ya dawo daga course ɗin sannan ya ƙara da cewa wai idan ta samu wani tayi Aure ta kawai. Toh kaga wannan alama ce ta ya janye hannunsa akan neman Aurenta kuma ga Alqasim mahaifin ƴaƴanta yana bibiyarta tayi haƙuri ta koma kan ƴaƴanta ta riƙe ƴaƴanta ta bawa ƴaƴanta tarbiyya da kanta shi yafi mata Al'khairi ”. Numfashi mai nauyi yaja kana ya ɗago idanunsa tare da cewa. “Abba nayi al'ƙawari zanyi mata magana kuma in Allah yaso ya yarda zaka ga sauyi”. Cikin jin daɗi da samun sassauci Abba yace. “Toh Allah yasa adace”. Cikin sanyi da rauni ya sake sunkuyar da kansa tare da cewa. “Ameen ya hayyu ya ƙayyum”. Abba kuwa Idanu ya zuba masa yana mai tuna mafarkin da Dadeey ta faɗa masa tsakanin Taj da Ishmah cikin sauri ya kawar da tunaninsa Aransa yace. “Ai mafarki ba gaskiya bane”. Nan dai Yah Muhammad ya shigo sukayi hira dashi. Bayan an idar da sallar Isha'i Ishmah da Tajuddeen ne aharabar gidan agarden amma ba ainihin cikin garden ɗin ba suna daga farko ƙasan Bishiyoyin ayaba yana zaune tana masa Video fuskarta ɗauke da Murmushi kana tana mai jujjuya fararen idanunta acikin nasa tace. “Kayi karatu mana kayi karatu”. Ƙwayar idanunsa ya juya kamar yanda takeyi yace. “Toh wace surah zan karanta Miki?”. Tana mai gyara wayar tayi Murmushi tare da cewa. “Ni kowanne ma ka sani ina so in dai acikin muryar kane tana yimin daɗi”. Ɗan murmushi yayi tare da faɗin. “Toh Bismillah”. Camerar ta saita akansa tana mai cigaba da Murmushi dake bayyanar da fararen haƙoranta. Shi kuwa Taj anutse yake kallonta tare da motsa lips inshi yace. “Dawo nan kusa dani”. Sai kuma ya maida kallonsa kan Laylah Minat dake can gefe tare da cewa. “Laylah!, Laylah!! Zo ki riƙe wayar”. Da sauri Laylah tazo ta amshi wayar video ta fara. Miƙewa yayi tare da ɗan gyara tsayuwarsa, a hankali itama Ishmah ta mike ta matsa kusa dashi kaɗan. Sai kuma ta kallesa shima kallon ta yayi kana ya ɗage mata girarsa ɗaya tare da faɗin. “Ya dai?”. Tana tura baki tace. “Ashe dai ka fini tsawo?”. Murmushi yayi wanda ke sake fitar da kyawun fuskarsa yace. “Ohhh dama ke tunani kike dama tsawon ki ya kai matakin da zaki iya kamani atsawo?”. Narkar da Idanu tayi kana tayi Murmushi tare da cewa. “Aini nayi tunanin baka fini tsawo ba”. Hannunsa ya ɗan ɗaga kana ya ɗaura saman akanta.. Laylah kuwa murmushi take tana cigaba dayi musu Video Minat ma murmushi takeyi. Shi kuwa Taj kuwa murmushi yayi cike da aji yace. “Kalli fa zan iya daura plate akanki inci abinci”. Ware idanunta tayi tare da faɗin. “Lallai dai kam haka kace amma idan na sa hill ai bazai yi ba”. Lallausan sajensa dake ƙyalli da sheƙi ya shafa kana yace. “Um-um ai ko kin sa bazaki gagareni ba dole dai kece a ƙasa na”. Sai kuma ya gyara tsayuwar sa tare da yin Bismillah Laylah kuwa cikin sauri tayi serving wannan video ta sake farawa daga farko wanda ba ƙaramin kyau sukayi ba. Ita kuwa Ishmah shiru tayi tare da tsura mishi ido, tana mai sake mishi lallausan murmushi. Kallonta yayi tare da faɗin. “Wacce surah kike so in karanta Miki?”. Sanyayyan numfashi ta fesar kana tace. “Aini kasan cewa kowacce surah ce ina jin daɗin saurara”. Murmushi yayi cikin jin daɗin yanda take son muryansa yace. “Ok bari in karanta Suratul Rahman”. Cikin jin daɗi tace. “Masha Allah Ubangiji ya mana Rahma arayuwar duniya da kiyama”. Ameen ya amsa kana ya fara karanta Suratul Rahman. _“Alrrahman”_ Ahankali Ishmah ta lumshe Idanunta tana mai motsa laɓɓanta. Shi kuwa cikin sanyayyan sauti mai sanya nutsuwa azukatan dake saura ya cigaba da cewa. _“AAallamal Ƙur'an”_ Ahankali ta buɗe idanunta dake lumshe ta zuba masa tana jin wani irin nutsuwa na ratsa ko wani ɓargo da tsokar da jinin dake gudana asassan jikinta. Kallon gefen Idanu ya mata tare da faɗin. _“Khalaƙal Insaan”_. Wannan karon kam kasa jurewa tayi haka nan taji alamar idanunta nason tsatstsafo da ruwan hawaye yayin da wani irin salama da aminci ke baibaye ta... Haka ya riƙa jero ayoyi dake ratsa zuciya. Dai-dai lokacin kuma Aunty Nana ta fito harabar gidan da alamu zasuje unguwa ne dan ga Khalid da Yah Muhammad har zata shiga mota ganinsu yasa tayi Murmushi tare da kallon mijinta da yake gaisawa da Taj ɗin. cikin girmaman darajarsa da kwarjin hasken Alqur'ani tace. “Barka da dare Sheykh”. Cikin sanyinsa cike da kamala ya ɗan risinar da kansa yace. “Aunty Nana Barka da fitowa”. Tana murmushi tace. “Barka dai al Sheiky bari muje Unguwa”. Yana kallon Ishmah yace. “Sai kun dawo”. Kai ta gyaɗa kana ta shiga mota, da sauri Minat ma tabi bayansu . Ahankali ya maida kallonsa kan Ishmah tare da cewa. “Gobe in Allah ya kaimu da safe zaki rakani gidan Hajja Umma in gaisheta, da Aunty Hawwa, Aunty Aysha, har ma da gidan Garkuwa inje in gaishe su ko”. Kai ta gyaɗa tare da faɗin. “Toh Allah ya kaimu lafiya”. Ameen ya amsa kana sukaci gaba da hirarsu. Washe gari da safe tsaye Ishmah take a kitchen ta jingina jikin sink ɗin kitchen numfashi ta fesar tana tunanin mai zata girkawa Taj na breakfast. Fridge ta buɗe ta ɗebo naman rago zallan tsoka ta wanke kana ta yanka albasa tare da saka maggi, garlic, curry, seasoning, sai ruwa kaɗan gass ta kunna ta daura tana tsaye ya tafaso kwashewa tayi ta zuba man gyaɗa cikin ƙaramin lokaci ya soyu bata barshi ya soyu sosai ba ta kwashe kana ta ɗauko plantain data yayyanka ta zuba acikin man cikin mintunan da baza su gaza uku zuwa huɗu ba ya soyu kwashewa tayi ta zuba wani shifter kana ta rage yawan man daidai yanda zai mata ta saka Tafarnuwa, Citta, albasa, jajjageggen attarugu da tattasai da ya wadatu da albasa ta zuba, sai kuma ta zuba curry, Maggi, da sauran spieces sama-sama ta soya kana ta kawo soyeyyen plantain da soyeyyen naman ta zuba bayan ya ɗan fara soyuwa ta kawo ruwan data tafasa naman kaɗan ta zuba sai kuma grean beans da Carrot ta zuba kaɗan sai ta ɗan watsa kifin data gyara a ciki tare da zuba yankekken albasa mai ɗan dama a ciki... Da sauri ta juya jin Aunty Nana da Aunty Maryam suna haɗa baki wurin cewa. “Masha Allah me ake girka wa wanda ya cika gidan da ƙamshi haka?,tun ina Azkhar ƙamshi ke barazanar toshe min hanci”. Murmushi tayi ita kanta tasan cewa source ɗin yayi masifar daɗi ga ƙamshi na musamman dake fita. Tana sauƙe tukunyar tace. “Laaaa Aunty Nana ba wani abu bane mai wahala bafa sai daɗi na yiwa Taj source da farar taliya kinsan bai fiye son abu mai nauyi ba”. Ta ƙare maganar tana zuba source ɗin cikin warmer me kyau wanda tuni ta juye farar taliya data fara da fawa acikin ɗaya Warmers ɗin murmushi Aunty Maryam tayi tare da cewa. “Aikam dai yayi kyau sosai ni kuma da har nayi mishi Chickensandwich da ɗan Yam balls. Ta kai ƙarshen maganar tana ajiye mata food flack's ɗin a gefentan. “Eh ai bai ɓaci sai ya ci abinda yakeso”. Ta faɗa tana kallonsu ganin yadda suke mata wani irin kallon tuhuma. “Kallon nan fa to?”. Kai Aunty Nana ta jujjuya tare da cewa. “Wai ku yarda cewa son juna kukeyi. Amman kunƙi yarda, sai randa so ya fasa muku zuƙata zaku gane”. Sai kuma ta kalli Maryam dake cewa. “A haka dai nasan ba wani ɗa na miji da zai iya samun zuciyarki muddin kina tare da Taj, na kuma tabbata shima ba matar da zaiso sama dake, mutumin da shine ya Kore min Yah Kamal ɗina”. Fuska ta kwaɓe tare da cewa. “Ba dama ayi abota da aminci sai mutane sunce soyayya ake, ni da Taj fa ba wannan mgnar.” Haranta kawai sukayi kana suka fice. Ita kuwa cikin nutsuwa ta haɗa masa kunun madara wanda yayi masifar kyau da daɗi kana yayi fari bata sa sugar da yawa ba tana saukewa ta koma bedroom wanka tayi kana ta shafe jikinta da Humra da kuma Kolaccar da Garkuwa ta bata towel ɗin ta since kana ta shirya kanta cikin wata atamfa mai golden dark green da ratsin maroon,sai kuma ratsin fari-fari da golden sosai rigar ya zauna ɗass ajikinta ɗauri mai V tayi kana ta ɗan ja ɗankwalin baya hakan ya bawa tattausan sajenta na gefe da saman goshi damar fita. Maroon gyale da plat shoes shima maroon ta sanya sosai tayi kyau duk da cewa ba tayi wani makeup ba amma asalin kyawunta ya bayyana baza kace ta Haifo ƴaƴa uku ba. Anutse ta ɗauki Basket data shirya ta nufi BQ da yake bakinta ɗauke da sallama ta shiga Falon. Zaune ta hangosa kan 3sitter kunnensa maƙale da waya. Ishmah kuwa cikin tsananin yaba kyawun da yayi ta motsa laɓɓanta tare da faɗin. “Masha Allah jinjina ya tabbata ga Ubangiji daya tsara wannan halitta mai cike da tsantsar nutsuwa da kamala sosai ta shagala da kallonsa sanye yake cikin wata Gezner Fara ƙal anyi masa ɗinkin riga da wando ƴar ciki da gariya irin na samarin zamani kansa na sanye da hula Mai mala yayin da ƙafarsa ke sanye cikin wani takalmi mai yatsa irin ratsin hular sajensa ya kwanta sai sheƙi yake alamar yana samun gyara yayin da jikinsa ke fitar da sanyayyan ƙamshin turare sosai ta shagala da kallonsa. Agefen Taj kuwa tun lokacin daya ji Sallamar ya katse kiran kasancewar ya gama magana yayin da ƙamshin Humra da Kwallaccar ya daki hancinsa yana masifar son ƙamshin jikinta sosai kwalliyarta ya ƙawatar dashi... Cikin sanyayyan Muryarsa yace. “Wa'alaikum Salam Ishmah”. Dogon numfashi taja kana ta janye idanunta daga kansa tace. “Taj sorry na Barka kana jira”. Ta ƙare maganar tana ajiye Basket ɗin kan dining sai kuma ta zauna a lokacin shima ya karaso zama yayi kan kujerar dake facing ɗin ta. Mikewa tayi ta ciro Warmer tare da ɗaukan plate ta zuba masa farar taliya da source, sai kuma ta ɗan sa mishi yam balls and chicken sandwich a Plata ɗaya cikin sauro ya lumshe idanunsa kana ya buɗe tare da cewa. “Masha Allah Ishmah wannan ƙamshin girkin ma kaɗai zai wadatar dani ba tare da naci ba”. Ware idanunta tayi tana Murmushi tace. “Um-um kadai ci”. Ta ƙare maganar tana ajiye masa plate ɗin gabansa sai kuma ta ɗan kalli fuskansa jin ya cewa. “Mu da muka zo gaisuwa, Amman duk kin kiwacemu mun zama kamar kajin gidan gona, naga Laylah tayi ƙiba sosai, ni ma ɗin so kike in zama ƙato ko?”. Murmushi tayi tare da Ciro Flaks ta da mug ta zuba masa kunun madara kana tace. “Eh ai banso Meymey taga gazawata mijinta ya koma a rame”. Kai ya jinjina yana tunanin wayar da yayi yanzu da Uncle Jibirin, dake cemai Meymey nata kuka wai ya tafi ya barta ya ɗauki Laylah ya barta da kewa. Sai kuma ya ɗan ɗauki fork ɗin, jin tana cewa. “Kaci mana”. Lokacin daya Kai spoon ɗin farko bakinsa sai daya lumshe idanunsa saboda daɗi da dandano daya ratsa harshensa Ishmah kam murmushi tayi jin yanda yake yaba girkin. Lokacin daya sha kunun madarar kam dariya tayi sosai jin yace sai ta koya masa dan sosai kunun yayi mishi daɗi. Bayan ya gama suka fito farfajiyar gidan dai-dai lokacin wayarta ya ɗauki ruri anutse ta duba ganin sunan Dr Nafi'u yasa tayi picking tare da kaiwa kunnenta bayan sun gaisa yace. “Kina gida ne?”. Kai Ishmah ta jujjuya kamar yana gabanta sai kuma tace. “Eh amma kuma yanzu zan fita”. Kai tsaye yace. “Ina zaki je?”. Tana gyara rufin gyalenta kana ta ɗan gyara zaman wayar akunnenta tare da faɗin. “Zan raka Taj wajen Hajja Umma ne”. Murya acun kushe yace. “Ok fita da shi yafi jirana muhimmanci ne?”. Ya ƙare maganar yanajin anya zai iya haƙura da ita kuwa, duk da baya son raɓa mata cutar dake tare dashi yanajin kuma son ɗanɗanar jinkinta, a ranshi yake faɗin. “Gwara a ɗaura mana aure mu tafi tare, tunda yanzu kwana arba'in ya rage in tafi, ai nima gani ina raye, so itama bazata mutuba sai muyi ta shan magani a tare”. Ya ƙare maganar zucin yana mai wassafo surarta a idon zuciyarsa. Ita kuwa Ishmah Ahankali ta juya ta kalli Taj. Taj kuwa fuska ya tsuke kasancewar yana ɗan jiyo abinda Dr Nafi'u ke faɗa. Ganin yanda Taj ya tsuke fuska ne yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da cewa. “Dr kamanta ance baƙonka annabinka”. Da dan fusata a Muryarsa yace. “Eh ban manta ba amma Allah da girma yake Miji da girma yake kin manta cewa Annabi Muhammad (S.A.W)yace da zai umarci wani yayi wa wani sujjjada a duniya daya umarci mace da tayiwa mijinta sujjjada”. Sanyayyan numfashi ta sauke kana tace. “To ai Dr ba'a riga da an ɗaura ba ko Dr?” . Cikin fushi da kishi yace. “Ohhhh gadarar da kike kenan ba'a ɗaura ba kin mance mungama komai har Sadakina yana hannuki, ke nifa na tsani wannan Taj ɗin naki da wasu makiran idanunsa na jarababbun maza”. Cikin sanyi da kuma son kawo karshen maganar tace. “Dr idan ya tafi dai shikenan”. Cikin fushi yaja dogon tsaki tare da cewa. “Idan ya tafi shikenan?,Ba shikenan ba idan kina so ki bishi sai in tabbatar daya fini matsayi da kima awajenki”. Yana kai ƙarshen maganar ya katse kiran. Cikin sanyi da rauni ta juya wayar nata ta kalla sai kuma ta kalli Taj. Taj kuwa hannunsa ya buɗe alamar ko oho kana ya nuna mata hanyar tafiya anutse yace. “Mu tafi mana”. Araunane ta kallesa sai kuma ta langwaɓar da kai tare da faɗin. “Taj fushi yayi fa”. Idanunsa ya lumshe kana ya buɗe su akanta cikin nuna mata matsayi da kima da take dashi awajensa yace. “To sai me Ishmah? Idan yayi fushi dake ai ba Abba bane yayi fushi dake, kuma bani bane nayi fushi dake, so kada ki damu, da ace duk duniya zasu juya Miki baya ni ina tare dake. Idan duk duniya babu mai tsaya miki Ishmah! Ni zan tsaya miki Idan duk duniya zasuyi ƙoƙarin saka ki hawaye Ishmah!Ni zanyi ƙoƙarin tsayar da hawayenki”. Lokaci ɗaya taji wani irin nutsuwa da farin ciki na maye gurbin da damuwar da Dr Nafi'u ya sanya mata haka nan taji zuciyarta ta aminta da duk wani abu daya faɗa ta san shi mai gaskiya ne bazai taɓa yi mata karya domin yasata farin ciki ba Taj kuwa Ahankali ya cigaba da cewa. “Kisa aranki idan kina tare dani ba zakiyi baƙin cikiba ki kuma sa aranki kin ƙulla alaƙa da farin ciki kada ki damu da fushin da yayi. Nasan kishi yake toh ya kwantar da hankalinsa shi yayi Sa'a ma ya kai matsayin mutumin da ake kallonsa amatsayin wanda za'a iya rayuwar Aure dashi ai Ni matsayina bai wuce matsayin Bestie ba”. Ya faɗi maganar daya fito daga ainihin ƙoƙon zuciyarsa. Jin yanda ya kai ƙarshen maganar yasa ta kallesa cikin gaskiya da gaskiya tace. “Ai matsayinka ya wuce matsayin Bestie Taj”. Cikin sauri mai haɗe da nutsuwa da kamun kai yace. “Toh matsayina matsayin meyene in ya wuce Matsayin Bestie?”. Murmushi tayi tare da cewa. “Matsayinka ya zama matsayin ɗan uwa tamkar Yah Muhammad haka nake ganinka Taj”. Gajeren tsaki yaja tare da cewa. “Hmmm mu tafi”. Kai ta gyaɗa kana suka nufi mota ta shiga mazaunin Driver yayin da ya zauna gefen mai zaman banza. Ta kunna motar anutse take driving ɗin yayin da yake gefenta azaune. Ahankali ya kalli zara-zaran yatsunta dake kan stearing tana juyawa numfashi ya fesar tare da cewa. “Ki ƙara gudu yanda kike tafiyar nan yaushe zamu isa? Dan Allah ma bani inja motar nan”. Ya kai ƙarshen maganar yana mai lumshe idanunsa tare da shaƙan ƙamshin humranta daya cika motar Kallon yanda ya lunshe idanunsa tayi sai kuma tayi Murmushi tace. “Tajjjj Um-um Ni zanje ka kifar damu”. Idanunsa dake lumshe ya buɗe tare da faɗin. “Ban gane in kifar damu ba kamar wani kasko”. Murmushi tayi kana tace. “Yanda ka saba gudu da jirgi in baka mota kaje ka tsinke min stearing mota Ni ba ruwana ina tsoro mu tafi ahankali”. Murmushi kawai yayi ya maida kansa jikin motar ya jingina tare buɗe lips inshi a hankali yace. “Hmmm ai kuwa duk abinda zanja innsarrafa bazan barshi ya sararaba”. Bata ji me yace ba, haka yasa taci gaba da tuƙin. A haka suka isa gidan Hajja Umma sun sha hira kafin ya tafi bayan ya mata Alkhairi mai wuyar mancewa, daga nan suka wuce gidan Ummominta da gidan Uncle Naseer da Uncle Ali gidan Garkuwa ce karshen zuwa sosai tayi farin ciki da zuwa su kana tayi musu tarba na musamman sosai ya yaba da karamcinta duk anan suka fi daɗewa kafin daga bisani sukayi mata sallama suka tafi... Ƙarfe 11:00 AM suka dawo gida. Wanda kuma 1:00 AM jirginsu zai tashi daga Yola zuwa Abuja. Ƙarfe uku na yamma kuma jirginsu zai tashi daga Abuja Nigeria to Addis Ababa Ethiopia. Kasancewar su Yah Muhammad,Yah Sadik, Adam, Hamisu sun san yau zai tafi, kana yau ɗin week end ne yasa basu fita ba har ma da Adam da yake ɗan kasuwa bai fita ba. Duk suka tsaya suka sallamesa cike da kewar juna. Sosai Abba yasa akayi masa addu'oi masu yawa tare dayi masa Godiya cikin jin daɗi da mutunta juna suka rabu... Misalin sha biyu saura kwata duk tsaye suke a harabar gidan. A hankili ya ɗan rusuna ya shafa kan Khalid tare da cewa. “My boy kace, pilot kake son zama ko?”. Cikin da sanyi yace. “Yess Uncle Taj ina so in zama kamar kai!”. Cikin so yace. “In sha Allah kuwa zaka zama pilot my boy kaine zaka zama magajin Uncle Taj”. Ya ƙare maganar yana shafa kansa tare da girgiza mishi kai ganin idanun yaron ya cika da hawaye. Sai kuma ya ɗan riƙo hannun Mahmud tare da cewa. “My son kace kai kuma Doctor kakeson zama ko”. Cikin kunya yace. “Eh Uncle Taj”. Yana mai jawoshi jikinsa yace. “Baka da matsala kana gama Secondary School zan kaika India kayi karatu a can, kana gamawa kujeran aikinka a AL-AHLI Afisha Hospital Qatar na jiranka”. Sai kuma ya kalli Minat yace. “Kefa My Daughter?”. Tana ɗan ƙara ruggume Laylah tace. “Uncle Taj nida Laylah duk medicine mukeso muma”. Kusan duk tare sukayi dariya. Abba ne yace. “Kun zama family Doctors and pilot's kenan”. Ya ƙare maganar yana shafa kan Laylah tare da cewa. “Laylah zamuyi kewarki”. Tana ɗan matse hawaye tace. “Abba nima zanyi kewarku”. Sai kuma suka kalli Hamisu dake cewa. “Toh Laylah mu zauna mana”. Da sauri ta kalli Taj tare da cewa. “Uncle Taj kace mishi yayi haƙuri nayi kewar Ummeey shiyasa zanmu tafi”. Yah Muhammad ne ya ɗan kallesu tare da cewa. “Lokaci ya tafi fa”. Shi kuwa Taj ta gefen ido ya kalli Ishmah dake jingine da motarta tayi ƙasa da kanta ko ƙala bata ceba. Sai kuma duk suka fara amsawa da Amin Ya Allah. Jin Abba nata jero addu'o'i. Aunty Maryam da Aunty Nana ne suka buɗewa Laylah marfin mota na baya ita da Minat da Khairat suka shiga Khalid da Mahamud kuma suka zauna a gaba kusa da Ya Muhammad. Ishmah kuwa driving set ta zauna yayinda Taj ke gefen mai zaman banza ɗin. Da kanta take driving suka nufi airport. Yayin da Yah Muhammad yake gabansu tana biye dashi a baya. A hankali Abba ke binsu a baya yana mai jero masa addu'a da godiya har suka fice a gidan. A hankali tasa hannun ta ɗan ƙara volume ɗin Radio cikin motar, a hankali ya ɗan juyo ya kalleta dai-dai lokacin da suka hau kan titin Airport “Ishmah!”. Ya kira sunanta a hankali. Bata amsaba kuma bata juyo ta kalleshi ba. A hankali ta ɗan juyo idanunta dake cike da ruwan hawaye jin ya kirata da wani sabon suna. A hankali ya ɗan juyo jikinsa duka ya fuskanceta tare da motsa lips inshi a hankali yace. “Maeeshah!”. a hankali ta ɗan taune gefen lip inta na ƙasa. “Yau kuma kece da kunna kiɗa harda ƙure volume”. A hankali ta gyaɗa mishi kai murya can ƙasa tace. “Kayi hakuri ai bani na sakaba gidan Radio Poolaku ne suka saka”. Ta ƙare maganar tana kai hannunta kan Radio alamun zata kashe a hankali yace. “Me ake faɗa a waƙar ɗan fassara min”. Cikin sanyi tace. “In fassarama da fillancin ko da larabci”. Yana mai ɗan lumshe idanunsa yace. “Da fillanci” Dai-dai lokacin kuma aka iso kan baitin da mawaƙiyar ke cewa. “Kaga komai za'a bayar dan ya zama fansar ma ɓoyar sonka bazan ambata ba”. Sai kuma ta ɗan ƙara volume ɗin tare da ɗan ƙara gudun motar tare da ci gaba da bin waƙar. “Da ace so zahiri ne, sai yazo mana baɗininini abinda nakewa duba”. Sai kuma tayi saurin juyowa tana kallonsa dai-dai lokacin data karya kwanan shiga cikin Airport ɗin jin ya amshi baitin waƙar da cewa. “Najeeh zance naki dai-dai dana cikin rai nawa sai dai. Ni bazaiyiwu na ambata ba. Zan kiraki masoyiyaa ko ince zinariyaaa, kin zamanna idaniyata ko meye ke zaki hango”. Ya ƙare baitin waƙar da lumshe sexy eyes dinsa da sunka sauya launi. Ita kuwa Ishmah a hankali tayi parking dai-dai lokacin da suka iso bakin mashigar matafiyan, sai kuma ta ɗan juyo tare dayin guntun murmushi kana tace. “Ka zamanna idan ganina ko meye kai zaka hangoooh”. Ta ƙare ajiye baitin waƙar tare da share siraran hawayenta da sunka zubo. A hankali yasa hannunsa tare da kashe Radio, sassayan numfashi mai nauyi ya fesar tare da shaƙan sanyin Ac da ƙamshinta. “Kin mance kin fassara min waƙar tun randa naga kin sakashi a status naki”. Kai ta jinjina mishi alamun ta tuna. Sai kuma duk suka gyara zama tare da fuskantar juna. Dai-dai lokacin kuma Yah Muhammad dasu Laylah duk suka shiga cikin holl ɗin yayinda Mahamud da Khalid ke jan trollings insu Taj ɗin. Agogon hannunta ta ɗan kalla tare da ɗan juyowa ta kalleshi kana a hankali tace. “Saura 40 minute ku tashi”. Sai kuma ta ɗan jingina kanta da jikin kujerar murya can ƙasan maƙoshinta tace. “Taj”. A hankali yace. “Na'am Maeeshah”. Ido na cikowa da hawaye tace. “Taj yanzu in ka tafi sai yaushe zan sake ganinka?”. Jingina kansa yayi shima tare da ɗan lumshe idanunsa kana yace. “Duk sanda kike son ganina, ki gaya min Maeeshah zanzo ki ganni kinji ko”. A hankali ta gyaɗa kanta dai-dai lokacin kuma hawayenta suka kwaranyo kan kuncinta. Zuwa yanzu shima kansa ji yake, tamkar ya saki kuka ko zaiji sauƙin suyan da zuciyarsa keyi a hankali yace. “Meyasa kike kuka Maeeshah?”. Murya na rawa tace. “Zanyi miss inka over Taj, na rasa Daddy na, kazo ka cike min rabin gurbinta, yanzu kuma kaima zaka tafi, ƙasarku ban san yaushe zan ƙara ganinka ba”. A hankali ya motsa lips inshi tare da cewa. “In sha Allah nine zan cike miki gurbin rashin Daddy baki ɗaya, muddin na samu dama bazaki sake zubda hawayen kiba, zan hana maraici raɓarki, zan nesanta zuciyarki da damuwa zan kusantata da farin ciki.” Ganin Yah Muhammad ya ɗan ƙonƙosa musu glass ɗin metarne yasashi buɗewa. “Ka fito an gama komai”. To yace kana ya ɗan ɗaga glass ɗin. “Aysha!”. Ya kirata da sunan da bai taɓa kiranta da shiba. “Na'am”. Ta amsa tare da bashi dukkan nutsuwarta. Gyara zamansa yayi da kyau tare da fara mata dukkan bayanin da Abba yayi mishi a kanta sai kuma ya ɗaura da cewa. “Dan Allah Aysha kisa Abba farin ciki, ki fitar da masoyin zuciyarki, kiyi aure domin shine cikar daraja da kimar duk wata ƴa mace, ki rabashi da zargin mutane da suke masa kallon shi ya sangartaki, yace ince miki bashi da wani buri a duniya daya wuce ganin kinyi aure, ya ƙara da cewa baya son Uncle Bello ya dawo yayi miki auren dole, shiyasa yace in faɗa Miki in da hali ki koma gidan su Khalid ki riƙe yaranki”. Ya ƙare maganar murya na rawa hawaye na zubo mishi. Yayinda itama tuni take zubda hawayen murya cike da rauni tace. “Taj kaine kake cewa inyi aure, in koma gidan su Khalid”. Kawai sai ta saki shesh-sheƙan kuka mai cike da rauni da abinda ita kanta bata san menene shiba. Yah Salam shine abinda ya iya furtawa saboda jin yana loosing confidence inshi duka har ya gaza control ɗin kansa. A hankali ya kai tafu kan hannunsa ya tallabe fuskantar cikin sanyi ya fara sharce mata hawaye da manyan yatsunsa yana faɗin. “So sorry don't cry Maeeshah”. Jin ɗumin tafukan hannunsa ne yasa bugun zuciyarta dai-dai har ya bawa hawayenta damar tsayuwa. Hango Yan Muhammad na taho garesu ne, yasashi saurin janye hannunsa daga tallabe fuskantar da yayi sai kuma ya miƙa mata hannun alamun so yake suyi musabaha. Cikin sanyi ta nuna mishi sama da idanunta alamun Allah ya hana. Cikin sanyi ya jujjuya mata kai still bai janye hannunsa ba... Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma sdw, da dai sauran abubudann ban lissafa Sune manyan alamomin infection. Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi. Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa. KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa. INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki. Idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA. Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh ai duk nisan state da kike ba ruwan mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in kinsan Baki shirya sayan kaya ba kuyi haƙuri kada kumin mgnar ku bari sai kun shirya,kada kuzo mu ɓatawa juna lokaci Allah y sni na tsani harkar ƙranta🙈🤗🤣, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi dka. By *GARKUWAR MARUBUTA* [1/14, 11:37 AM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 12* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin INDA RAI na kiɗine yanzu free pages ne mukeyi kuma saura ƙiris su ƙare 1k ne kacal yar uwa ki saya ki karanta cikin aminci 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276, Gareku Mutanen kasar Niger +22790899076 Ga number da zakuyiwa magana ta wurin Mommy zaku biya 1000fc jaka ɗaya kenan rak zaku tura mata* *Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan, Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace butar sirri, furar mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k ragayar alkhairi 13k 10k shine ƙarami haɗina na karshe sai kuma haɗin robar ƙasaitacciyar shi 5k ne shine ƙarshen haɗina kenan... Manyan set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi* “Saura 30 minute fa ku tashi”. Ya Muhammad Ya faɗa. Cikin sanyin jiki yace. “Okay ina zuwa”. Kai ya gyaɗa kana ya koma ciki, ganin dafa gaske bazai fita bane yasa ta miƙo mishi hanunta, a hankali ya haɗe tafukan hannunsu wuri ɗaya tare da lumshe idanunsa da suka sauya launi murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Idan ina tare dake ji nakeyi duk abin da nake muradi na duniya yana tare dani, in nayi nesa dake ji nake bani da farin ciki, bayan iyayena ba fuskar da nake gani inji daɗi sai taki. in gani gaki sai inji ina farin ciki ya mai sabuwar amarya”. Ya ƙare maganar lips inshi na rawa tamkar maijin sanyi. Ita kuwa Ishmah tuni jikinta ya saki rawa. Da sauri ta janye hannunta kana ta naɗeshi cikin gyalenta. Shi kuwa Taj a hankali ya buɗe marfin motar kana ya fita. Binshi a baya tayi, suna shiga yayi sallama da Yan Muhammad da yaran kana ya kama hannun Laylah suka shiga inda zai sadashi da wurin jirgin. Su kuwa suka juya gida cike da kewar Laylah da Uncle Taj ɗin. Ƙarfe ɗaya dai-dai jirginsu ya tashi zuwa Abuja. Biyu saura 13 minute suka sauƙa a Abuja. Sallan azahar sukayi tare da cin pepper chicken da Ishmah ta haɗa musu, tare da shan Yoghurt fruit data haɗa musun. Biyu dai-dai jirginsu ya fara ƙugin tashi. A hankali yace. “Maeesha yanzu jirgin zai tashi zan bar ƙasar Nigeria cike ƙuncin zuciya domin ji nakeyi tamkar na bar dukkan farin cikina a ƙasar”. Cikin sanyi tace. “Taj nima ji nakeyi tamkar ka tafi da dukkan farin ciki na, rashin Daddy na ya dawo min sabo”. Daga nan dai sukayi sallama kana suka tashi sai Ethiopia....... Washe gari Ranar Monday zaune yake gaban Yah Abana da Ummeey sai kuma Mom Amal da Yah Hafiz yana basu labarin yadda ƙasar Nigeria take da irin karrama da ƙaramcin daya samu a wurin mutanen ƙasar More especially malam izala da ɗarika. Numfashi mai nauyi Malam ya sauke zuciya cike da saƙa yace. “Babana wanne state da wanne kaje?”. Gyara zansa yayi tare da cewa. “forko dai Abuja Adamawa, Borno, Zamfara, Kano, Bauchi”. Da sauri yace. “Har Bauchi!!?”. Kai Taj ya jinjina mishi tare dare da cewa. “Acan na samu wani dottijon malami Sheykh Tajuh Usman Bauchi.” Sai kuma duk ya basu labarin yadda sukayi da kana ya daura da cewa. “Yah Abana harda sandarsa ya bani yace in kawo maka, ni kuma ya bani alkyabbarsa harda rawaninsa”. Tunda ya fara bashi labarin Malam ya tsuke fuska tamkar bai taɓa dariya ba, babu wannan annuri da nuna soyayyar cikin sanyi Ummeeyshi kuma tace. “Babana kaci abinci mana”. Yana kallon sauyin fuskar mahaifin nasa yace. “Ummeey daga gidan Addawa nake fa, acan nayi breakfast”. Sai kuma ya kalli Mom Amal dake cewa. “Ya baka zo mana da Laylah ba?”. Ta ƙarashe cike da makirci, yana ɗan gyara zamansa yace. “Har zamu taho tare to, kuma ashe da zazzaɓi ta kwana, na bata magani na barta tayi bacci”. Wani irin makirin murmushi tayi tare da cewa. “Da alama dai Laylah itace ta biyunka, gashi tun kan ayi aure ta zama jakar ratayawarka!”. Cikin ƙyamata da nesanta da kalmar da tazo mishi a bazata, zuciya cike da girman matsayin da ya tsayawa Laylah na uba uwa dangi, da iyakar gsky yace. “Wa'iyazubillah Laylah bata cikin sahun matan da ya kamata ace kun siffantasu da haka, ni Laylah a matsayin ƴar cikina na ɗauketa, kuma jinta nake a jikina tamkar ni na haifeta, ni zan zame mata uba da uwa da yayun data rasa. Dan Allah Mom karki na kamanta wannan a zuciyarki!”. Ya ƙare maganar da iyakar gskyarsa. Ita kuwa Mom da sauri tace. “Toh ya haramta ne?”. Hannu Malam ya ɗaga mata tare da cewa. “Haba tunda yace abar mgnar ai sai mu barta ko”. Sai kuma ya kalli Taj ɗin tare da cewa. “Kace yau kana da tafiya zuwa Qatar ko?”. Kai ya jujjuya tare da cewa. “A'a American Passingers zan dauka, in na sauƙesu ne zan ɗauki na Qatar, daga Qatar ɗin zan juyo nan”. Kai ya jinjina tare da cewa. “Allah ya taimaka, ya batun aikin Asbitin da sa mishi suna”. Yana amsa Apple ɗin da Ummeeyshi ke miƙa mai yace. “Eh anyi komai an gaba duk abinda ya dace, an kai sabbin kayan aikinma”. Ya ƙare maganar yana dan murza Apple ɗin alamun da sauran abinda yake son faɗi. “Sunan fa Tajmuh hospital aka sa ko?”. Mom Amal ta tambaya. Ba tare da ya kalleta ba yace. “AL-AHLI AFISHA HOSPITAL”. Ya bata amsa a takaice. Da sauri tace. “To me yaci sunan Malam ɗin, kuma waye Sha ɗin kuma”. Yah Hafiz ne ya gyara zama tare da cewa. “Sobada wannan Hospital ɗinsa ne, na kanshi bana Malam ba babu ko asin malam a ciki, batun wani Sha kuma ai sirrinsa ne, tunda kin gane Afi ɗin firkon sunansa ne”. Wani mugun kallon ƙasa-ƙasa ta watsa Yan Hafiz ɗin. Shi kuwa Taj gaba ɗaya hankalinsa na kan sauyin mahaifinsa. Ummeeyshi kuwa murmushin jin daɗin bayanin Hafiz tayi yoh ai gwara su sani kada su ɗaurawa ɗanta jakar tsaba kaji su bishi su tsatstsageshi suce mahaifinsu na fifitashi, ita a burinta ma tunda Kabeer ya gama karatunsa tunda shina likita ya karanta zata sa Taj ya bar mishi ragamar Asbitin. A gidansu Adaya kuwa, cikin tsananin damuwa Abpu ya kalli Ummin Adayan tare da sauƙe numfashi mai nauyi kana ya kalli Ma'aruf tare da cewa. “Zuwa yanzu dai na fara tsinkewa da lamarin mutumin nan fa, yasa an ɗaura auren Adaya da ɗansa, yanzu mako huɗu cib har an shiga na biyar Amman shiru bashi ba alamarsa bare ɗansa”. Sai kuma ya kalli Ummin Adayan dake sauke ajiyan zuciya alamun tasha kuka. “Shiyasa ni banso ayi irin wannan aurenba, da barinta akayi ta zaɓa da yafi mana”. Ta faɗi tana zubda siraran hawayen. “Kayya Ummi ai dole ce tasa Abpu yiwa Adaya irin wannan bauɗeɗɗen auren saboda gudun lalacewarta da raye-raye nan data sawa ranta”. Cewar Ma'aruf. Cikin sanyi Ummin tace. “Toh yanzu me daurin auren ya hana, tun jiyafa data fita da Asina Izzin gata har yanzu bata dawoba”. Cike da damuwa Abpu yace. “Kema da laifinki, kin sake mata fuska yasa bata tsoron fita”. Da sauri tace. “Wallahi Allah kenan ba yadda banyi da itaba kada ta fita, Adaya ta fetsare wai tana cemin dolefa ta fita wai yanzu saura watannu su tafi gasar rawan da aza'ayi dan haka duk watannin nan na yin rihazal ne”. Cike da takaici Abpu ya miƙe ya fice daga Parlour. A hankali ya shiga Parlour Addawa, cikin sanyi ya zauna bisa kujerar 3 sitter, ɗan kishinƙida yayi tare da rumtsa idanunsa. Yau tunda gari ya waye yake ta kiran Ishmah bata amsa kiranshi yayi mata text message ba amsa, yayi mata mgn ta Whatsapp ɗin da tasan domin ta kaɗai yake yinsa ta buɗe ta kuma gani ba amsa. Ɗan gajeren tsaki yaja tare da juyawa rufda ciki yana lumshe idanunsa haka nan yake jin wani irin sassayan yanayi na gameshi a kanta. Addawa kuwa wacce tun amsa sallamarsa da tayi bata kuma cewa, komaiba haka shima bai kuma ce mata ko ƙalla ba. Shi yasa ta zira mishi idanu. “Lfy kuwa!?”. Kake ta faman jan tsaki”. A hankali ya ɗan yunƙura zaune tare saurin jawo wayar tashi jin kira ya shigo, a zatonshi itane, sai kuma yaga Aunty Rashida ne, cikin sanyi ya amsa kiran tare dayin sallama kana ya ɗaura da cewa. “Afwan Aunty Rashida jiys da dare muka iso, yau kuma kin san ranar Ummeyn da Yah Abana ne”. Shiru ya ɗanyi sai kuma yace. “In sha Allah zan zo, Amman yau zan tashi zuwa American, sai na dawo zanzo sai muje gidan Aunty Maryam ma”. Daga nan dai suka ɗanyi hira kana ya katse kiran, tare da tashi zaune jin Addawa tana ta mita. “Ba wanda ka rainawa wayo sai ni, ka ɗebo damuwa kazo kaƙi gaya min me matsalarka ka sani a damuwa, kaje ka tasa iyayen ka mana, wlh ina jiye maka tsoron shege zurfin cikin kan nan zai jaza maka matsa a rayuwar ka, yanzu menene kake yiwa tsakin?”. A hankali yace. “Ishmah ce”. Wani fahimtaccen murmushi tayi tare da cewa. “Me kuwa tayi maka”. Shafa sajensa yayi tare da cewa. “Yau tunda gari ya waye naketa kiranta, bata piking call ɗin na nayi mata text no raspond. Tun jiya da darefa da muka sauƙa ta kirani bata kuma kirana ba”. Numfashi mai sanyi ta fesar tare da cewa. “Toh da nake ce maka, bazaka iya rayuwa ba tare da itaba, ai gani kake kamar shirme tsufa ne, gani wuni ɗaya rak ne baka jita ba duk ka damu, sonta kakeyi sonka takeyi kuna ta yaudarar zuƙatanku in na faɗa gani kake bansan soba, alhalin kuma kaine nan baka san soba”. Kwaɓe fuska yayi tare da cewa. “Toh in ana son juna kuma sai aƙi ɗaukar wayan juna, Kinga ai da tunaninki hakanne da baza ta ƙi amsa kirana ba”. Da sauri tace. “Wata ƙil rashin nuna kana sonta ne yasa tayi fushi da kai, tukun nama daya kuka rabu ko ka mata wani laifi”. A hankali ya fara mgnar zuci da baisan tana fita ba. “Ni ba laifin da nayi mata, kawai dai nayi mata nasihar tayi aure ko dan sa mahaifinta farin ciki, domin ya shaida min baya jin daɗin zamanta haka”. Sai kuma yayi saurin kallon Addawa jin tana cewa. “Hmmm Allah ya kyauta, in tayi tsami ai kwa fitar da ita in kunji yana gab da kasheku”. A hankali ya miƙa mata hannunsa tare da cewa. “Bani wayarki”. Miƙa mishi wayar tayi tare da miƙewa ta nufi kitchen. Shi kuwa number Ishmah yasa tare da kiranta bugu ɗaya ana biyu ta amsa kiran. “Assalamu alaikum Addawa”. Cikin sanyi ji murya a narke yace. “Kiyi haƙuri dan Allah kada ki hukuntani, da nesanta kanki dani, kada ki hanani jin muryarka Please abotarmu bata cancanci hakaba Maeeshah”. Sassayan numfashi ta fesar tare da cewa. “Taj kainefa ka bani shawarar inyi aure ko?”. A hankali yace. “Ehhhh”. Tana mai rumtse idanunta tace. “Toh shiyasa na fara nesanta da kai domin in nayi auren ai bazai yiwu muci gaba da abotarmu ba”. Cikin wani irin damuwa yace. “Kin mance cewa, kince ni dake ba abota bace ƴan uwantaka ce”. Da sauri tace. “Amman ai duk da haka in dai nayi aure mgnar da mukeyi zata haramta”. Cikin sanyi murya yace. “Dan Allah ki bar mgnar nan Maeeshah ki bari in kinyi auren nayi miki alkawarin nida kaina zan nesanta dake, irin nesantar da bazaki sake jina da ganina ba”. Yayi mgnar da jin cewa kamar nesanta da ita zaisa ya nesanta da rayuwa. Jin yadda yaketa mgnar cikin sanyi ne yasa tace. “To ba matsala yanzu dai lokacin salla yayi sai anjima zamuyi waya”. Da sauri yace. “Kinyi al'ƙawari”. Cikin jin bazata taɓa yi nesanta da shiba tace. “Eh Taj nayi al'ƙawari zanci gaba da yin waya da bestie na”. Daga nan sukayi sallama. Ganin lokacin salla Magrib yayi yasashi yin al'wala ya wuce gidansu. Domin in yana gari shike limancin a masallacin kamsusul salawat na ƙofar gidansu. A daren ranar jirginsu Taj ya tashi zuwa America. Washe gari da safe, Meymey ce zaune a Parlour tallabe da kafaɗar Laylah daketa kwaza amai gaba ɗaya jinkinta yayi luƙus. Cikin nuna tsantsar kulawa tace. “So sorry, tashi mu tafi Hospital aman nan ya isa haka”. Cikin galabaita da muguwar kasalar da ta kwana dashi tun randa suka dawo Nigeria ta yunƙura ta miƙe. Da taimakon ta suka tafi Aabet Hospital. Bayan awa ɗaya da zuwansu ne suka fito kai tsaye gidan su Taj ta wuce da ita. A Parlour Ummeyn suka zauna. Bayan ta gaida Ummey cikin girmamawa tace. “Malam yana cikine”. Cikin kulawa da jin daɗi Ummey tace. “Eh yana ciki muje ko”. Ta ƙare maganar tana kallon Laylah dake kwance tayi luƙus sai kuma ta bita da ido ganin ta miƙe da sauri ta nufi Dinnin area. Yawu mai yauƙi ta ɗan tofar a washing hand baby dake Dannin area ɗin. Sai kuma ta dawo ta zauna, ita kuwa Ummeeyshi cike da mamakin irin wasu sauye-sauyen da ta gani tare da yarinyar ta miƙa mata hannun tare da cewa muje ku gaida malam.” Miƙewa meymey tayi tana mai ɗan latsa wayarta. A Parlour suka samu Mom Amal da Aryan sai Kabir. Suna shiga Mom Amal ɗin ta zuba wa Laylah idanu tana ƙare nazartanta. Ita kuma Laylah cike da azabebben kasalar data buwayi rayuwarta ta tsuke bakinta saboda yawun daya sake cika mata baki so take ta sake tayi ta bawa Ummeey labarin Ishmah dasu Minat da Rahma Amman ina duk ta rasa kuzarinta. Gefen Ummeey ta zauna tare da lafewa a jinkinta. Cike da tsananin mamaki Mom Amal tace. “Ikon Allah bag ɗin Taj ya haka saikace mai laylayin ciki”. Cikin tsananin sinkewar zuciya Ummeey tace. “Subahallahi wannan wacce iriyar mgna ce haka Mom Amal”. Ta ida mgnar tana kallon yadda Laylah ta sake. Aryan ne yayi saurin cewa. “Ai kam tayi kama da masu ciki”. Sai kuma ya kalli Kabir dake cewa. “Ni kuma gani nayi tayi ƙiba”. Ita kuwa Meymey tsuke fuska tayi tare da cewa. “Kai Mom ai sai kisa zuciyata ta buga in mutu da wannan mummunan hasashen naki akan, yar amanan tamu, Malaria 🦟 cefa ta kwatso a Nigeria wata ƙil harda taypot”. Dai-dai lokacin Malam ya fito daga dakinsa bisa dukkan alamu yaji duk abinda suke tattaunawa a kai saboda jin yana cewa. “Toh kin kaita asibiti ne Mamana?”. Cikin sauri Meymey tace. “Eh Malam yanzuma daga Hospital ɗin muke, kuma ta samu magunguna”. Cikin gamsuwa yace to Allah ya sauƙawa.” Da Amin suka amsa baki ɗayan. Bayan kwana biyar. Adaya ce tsaye a tsakiyar babban hall ɗin da suke ɗaukan darasin rihazal na gasar rawan da zasu tafi nanda watanni uku zuwa huɗu, wanda shine kaɗai babban burinta. Wani irin shu'umin waƙa da kiɗi rawarsu na Ethiopia's Gerls aka sake mata, yayinda itace jagorar tawagar shiyasa itace a gaba. Asina agefen damanta sai kuma Bititi a gefen hagu wacce ita arniyace. Sai kuma bayansu Izzin ne a gabanta sai wasu maza uku. Wani irin rawa sukeyi na kafaɗa da kaɗa ƙirji. Rawa sukeyi kai kace babu ƙashi a jikinsu. Shi kam Izzin rawar yakeyi cike da ficewar hankali sabo yadda ƙirjin Adaya ke hautsuna mishi lissafi, dan wani irin juyi da tsalle tantsama-tantsaman ƙirjinta ɗin sukeyi tamkar zasu rabu da ƙirjinta su zube ƙasa. Gigatashi da sukayi ne yasa ya sauya salon rawar tasu, da ƙara kusantarsu ta baya. Kana yasa hannun damansa ya zagaye lafeffen cikinta, tare da ɗaura na hagunsa kuma saman ƙirjinta. Haka suma sauran sukayi. Matse cibiyoyinsa yayi da masifar ƙarfi ya rinƙa tsalle da karya kafaɗarsa haka yasa itama bada ƙaimi, burinta yasa ta gaza tantance abinda yake mata, ya saɓa tunanin. Sauranma haka suke rawan. Yayinda couch da sauran fara yi musu tafi da ihu. Haka dai suka kwana wannan jarabar rawar. Koda garin ya waye a gajiye ta dawo gida. “Yanzu kenan Adaya ki rantse lalata rayuwarki zakiyi a banza ki zubda kima da darajarki na ɗiya mace kuma musulma”. Cewar Umminta hamma mai cike da bacci tayi tare da cewa. “Dan Allah ki bari in nayi bacci na farka zamuyi mgn”. Ta ƙare maganar da sake video da sukayi a TikTok. Sai kuma ta cilla wayar kan gado ta shigo Bathroom. Ganin haka ne yasa Umminta fita rai cike da ƙuna. Kwanan Taj takwas da tafi kafin ya dawo, gidansu ya fara wucewa kai tsaye saboda Ummeynshi ta shaida mishi Meymey da Laylah suna gida. Cikin mamaki yake kallon Laylah da tayi wani irin fari na fitar hankali har wani yellow-yellow tayi, musamman goshinta da yake wani irin ƙelli, kana tayi wata ƙibar da bai santa da shiba. Cikin mamaki yake lallonta sai kuma ya ɗan juyo ya kalli Meymey dake haɗa mata tea. “Yah Salam wai me yake damunta ne?”. Fuska a tsuke tace. “Ni ya kamata inyi maka wannan tambayar, tunda ni ba likita bace”. Cikin tsuke fuska yace. “Bana son mgnar banza, ba kece kika kaita asibiti ba”. Sai kuma ya ƙare maganar da jawo hannun Laylah yace. “Taso mu tafi Hospital”. Da sauri Ummeeyshi tace. “Yanzu fa suka dawo daga Asbitin”. Sai kuma ta kalli Zakiya dake miƙawa Laylah ɗanyen dabino irin mau gafin nan da tace tana so, cikin tsoro Ummeey tace. “Kai nifa al'amarin nan ya fara bani tsoro, duk fa abubuwan da Laylah keyi na masu juna ne”. Bai fahimci mgnar Ummeyn ba bare ya damu. “Zuwa yanzu dai nima na fara zargin da Mom Amal takeyi cewa Laylah nada ciki ne”. Baima jitaba bare ya fahimci me take faɗa. So kawai ɗaukar Laylah yayi suka tafi Hospital. Yayi mata ƴan gwaje-gwaje kuma basu ga matsala tare da itaba. Sai ɗan Malaria ɗin tsarabar Nigeria daga asibitin gidan Addawa ya wuce da ita. Kusan ƙarfe goma na dare ne Meymey ta kalli Ummeynshi cikin sanyi tace. “Hmmm kinga har yanzu bai dawo ba ko”. Kai Ummeey ta jinjina tare da cewa. “Bari in kirashi”. 3 miss calls tayi mishi Amman bai ɗauka ba. Shi kuwa Taj tuni sun koma gida shida Laylah ta wuce ɗakinta. Shi kuma ya wuce side ɗinsa. A zatonsa ma Meymey ta dawo. A Parlour ya zube woyoyinsa bisa senter table dake tsakiyar Parlour shiyasa baiji kiran Ummeeyshi ba. A hankali cike da alamun gajiya da kasala da nannauyan baccin da yakeji. Mai ya ɗan shafa kana ya fesa turare, ɗaya daga cikin tattausan towel nashi da sune na baccinsa ya zare tare da ɗaurawa a ƙugunsa. Bakin gadon ya zauna tare da yin addu'a ya shafa kana ya kwanta kamar yadda ya saba a rayuwarsa daga shi sai Towel ko jallabiya haka yake kwana. Yana kwanciya bacci yayi awon gaba dashi. Cikin sanyi Meymey tace. “Ummeey asa ko Kaber ne ya maidani dan nasan Yah Afif in dai yana tare da Laylah baya tuna komai”. Ta ƙare maganar da alamun takaici. Ɗan ƙwaffa Ummeey tayi kana ta kira Kabir ɗin yazo ya maida ita. Alhamdulillah yanzu kasalar da sauƙi sosai tunda ya haɗa mata magunguna sai yawune dai har yanzu. Bayan kwana biyu da safe. Laylah ce zaune kusa da Meymey a dinning table, magungunanta ta ɓare ta bata tare da miƙa mata ruwa. Amsa tayi tare da shansu. Fitowan Taj ne yasa ta ɗan zuba mishi ido cike da alamun da yafi kama da tsoro. “Masha Allah Laylah ya jikin”. Ya ƙare maganar yana sa hannunsa a wuyanta. Cike da tsananin tsoro ta sunkuyar da kanta murya na rawa tace. “Da da dasauƙi”. Cike da kulawa yace. “Ya dai Laylah me haka jikinki yake rawa?”. Da sauri tace. “B.. ba... Bab.. babu”. Ita kuwa Meymey idanu ta zuba mishi cike da alamun son gano wani abu. Dai-dai lokacin kuma kiran Ishmah ya shigo wayarsa. Amsa kiran yayi yana kallon Laylah da duk ta takure jinkinta. “Jikin Laylah da sauƙi Maeeshah”. Ya faɗa tare da motsowa kusa da Laylah kana ya miƙa mata wayar da faɗin. “Gata”. Wani irin kallon mai cike da tarin manufofi Meymey ke liƙa mishi. “Hello Aunty Ishmah”. “Na'am Laylah ya jikin naki?”. Cikin sanyi kasala da ya zame mata jiki tace. “Da sauƙi sosai ma”. “Masha Allah to Allah ya ƙara sauƙi kina cin abinci kiji ko”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “To Aunty ina Minat?”. Cike da kulawa tace. “Tana gidansu”. Daga nan dai sukayi sallama. Amsar wayar yayi tare da ficewa. Ya wuce Tajmuh hospital. Yana isa ya fara aikin CS ɗin da zasuyiwa kusan mata biyar, da taimakon Dr Farida da Dr Adey sukayi komai. Kwanan Taj goma da dawo kana ya sake wata tafiyar zuwa Bangaladash daga can ya wuce India Kwana shi biyar ya dawo Ethiopia. Yau tun safe kuma Laylah ta kuma tashi da amai da zazzafan zazzaɓi. Haka yasa ta ɗauketa tayi gida da ita. A Parlour Malam suka samu, mafiya yawan mutanen gidan. Bayan sun gaisa ne Meymey keyiwa Ummeey bayanin jikin Laylah, cikin taɓe fuska Mom Amal tace. “Na rantse da zatin Allah ƴannan cikine da ita, in kunƙi kuma kuje ayi muku gwajin cikin zakusha mamaki wlh. Cikin fara jin tsoro da ganin alamun gskyar Mom Amal Ummeyn tace. “Gsky dai nima ina gafa gwara aje”. Dai-dai lokacin kuma Taj dake shigowa yace. “Ba wani ciki a jikin Laylah dan Allah Ummeey ku daina faɗar hakan, hankali na tashi innaji kuna batun Laylah”. Ya ƙarashe maganar tare da zira wayar shi cikin aljuhun ba tare da ya katse wayan da yake yi da Ishmah ba. Kusan duk a tare suka juyi suka zuba mishi idanu. Malam kuwa wani irin kallon cikin ƙwayar idanun Taj ɗin yake tamkar mai son karantan wani abu. Ita kuwa Meymey cikin tsoro tace. “Gsky dai nima zanso ayi mata gwajin cikin nan, dan abin ya fara bani tsoro ayi kawai hankali na ya kwanta”. Maman Yah Hafiz ne ta jawo hannun Laylah tare da cewa. “Laylah meke damunki ne?”. Laylah da batama san menene suke mgn a kaiba jiki cike da kasala ta juya ta fita, yawun bakinta ta zubda kana ta dawo. Ita kuwa Maman Yah Hafiz cikin sanyi tace. “Dan Allah ku daina alaƙanta ƴariyar dake da alaƙa da gidanan da wannan mugun abun da bazamu iya ɗaukaba”. Ta ƙare maganar tana kallon Malam da ya kafe Laylah da kallon dake nuna tsananin tsana da ƙyamar da zata iya fuskanta a tare dashi, domin tasan yadda zuciyar mijinta yake farin sani. Yayinda duk sauran kuma suka zurawa Laylah ido murya a raunace tace. “Nima ban saniba, bana iya cin abinci kuma yawuna ba daɗi in na haɗiye amai nakeyi”. Da sauri Mom Amal tace. “To me kikeson ci?”. Tana zamewa kwance tace. “Abu mai tsami”. Yah Salam shine abinda Taj ya iya faɗa zuwa yanzu shima tsoro mai yawa ya rufeshi musamman da ya ƙura mata idanu a matsayin sa na likita ya gano alamun ciki. Cikin sauri duk suka kalli Malam da yaja wani firgitaccen numfashi tare da cewa. “Kai Hafiz ɗauketa ka kaita a gwada min ita yanzun nan nake jiran amsa”. Ya ƙare maganar cikin tsananin tafasowar fusatar zuci Da sauri Yah Hafiz ya miƙe. Meymey miƙewa tayi tare da tallabe Laylah kana suka nufi waje. Cikin so da kulawa Malam ɗin ya kalli Taj daya juya da nufin zai bisu. “Zo Babana ka huta, yayanka zai kaita, yanzu ka dawo ko ruwa baka sha ba”. Wani irin mugun kallo Mom Amal da Aryan suke mishi ƙasa-ƙasa. Mamin Aryan kuwa da ido ta tsare ɗan nata ganin kallon da yakeyiwa ɗan uwan nashi, cikin mmki da tsanan hali irin na Aryan ta miƙe ta bar Parlour. Nigeria Abba ne zaune a Parlour shi bisa dukkan alamu waya yakeyi da Yayanshi Bello. “Ya gajiyar ibada kuma”. “Alhamdulillah ai yanzu kam gajiya tabi lfy, yau wata ɗaya gudafa kenan da dawowarmu, in sha Allah ma nanda mako biyu dai ina nan tafe zan shigo Adamawa, ɗazu nayi waya da Ishmah nace mata ta shirya”. Cikin girmamawa Abba yace. “To Masha Allah, Allah ya kawo ka lfy, ba ruwana Kaida ɗiyarka”. Ya ƙare maganar cike da kara. “Ɗazuma ma Adam ke cemin wai ashe Dr Nafi'u ma, yabar ƙasar jiya ko?”. Yana gyara zaman hularsa yace. “Eh yace wai ta ɗan jirashi in ya dawo zasuyi auren”. Cikin faɗa Uncle Bello yace. “Bamuyi wannan alƙawarin ba, wlh ina zuwa Adamawa zan ɗaura mata aure, da duk wanda yake buƙata, idan kuma Mukhtar yace yana sonta wlh aura mishi ita zanyi. Dan yaron yana da mutunci dan koda na dawo Umrah yazo min sannu da zuwa”. Kai Abba ya jinjina domin ya sani tabbas. Mukhtar (Bappa Kawu) yana da mutunci da Kamala ko shi bazai ƙi aurenta da Mukhtar ba. A cikin gida kuwa. Cikin tarin damuwa Ishmah ke jin duk maganganun da akeyi a Parlour Yah Abana ta wayar Taj dake cikin aljihunsa. Ganin kiran Bappa Kawu ya shigo wayarta ne yasata katse kiran Taj ɗin kana ta amsa cikin sanyi tace. “Assalamu alaikum, Bappa Kawu”. Murmushi yayi tare da cewa. “Ni dan Allah na tuba a dena cemin Bappa Kawu nan ko Hamma ki kirani ba sai kince my price ɗin ba”. Cikin sauƙe numfashi tace. “Wannan ai tsohon suna ne”. Da sauri yace. “Ni kuma so nake a sabunta minshi, To my princess, ai ni so nake ki aminta dani fiye da amincin da kikayi dani a baya domin a yanzu da yaƙinin aure na dawo da ƙarfi na”. Cikin sanyi tace. “Bappa Kawu ka dawo ka kuma yin wasa da zuciyata kenan ko?”. Ta ƙare maganar tana jin son da tayi mishi a baya na tasowa. Allah ya sani taso Mukhtar rabuwan su haukane kaɗai batayi ba. Cikin salon so ya rinƙa isar da soƙonsa. Ethiopia. Kusan duk ma zauna Parlour ido suka zubawa Yah Hafiz da ya zauna gaban Malam yayi ƙasa da kansa hawaye na kwaranya a idanunsa. Ganin haka ne yasa Taj yin mutuwar zaune saboda koma menene yasan ba labari mai daɗi bane. Kana ga Meymey a durƙushe a gaban Malam ɗin tana sakin shesh-sheƙan kuka. Laylah kuwa jikin Ummeeyshi ta faɗa tana karkarwa. Ita kam Ummeeyshi tuni ta fara karkarwa. Mom Amal kuwa cike da zaƙuwa tace. “Hafiz mgn zakayi ba kuka ba, me likita yace?”. Ta ƙare maganar da kallon Malam da fuskarsa ta sauya daga fara zuwa jazir kana idanunsa sunka ƙanƙance suka kuma sauya launi daga fari zuwa fatsu-fatsi. Cikin Muryar dake nuna tsananin fusata da tashin hankali yace. “Hafiz me likita yace?”. Cikin raunin murya Yah Hafiz yace. “Dr yace tana da ciki har na tsawon wata uku”. Wani irin masifeffen harbawa zuciyar Taj tayi lokaci ɗaya zufa ya karyo mishi. Da sauri kuma ya rumtsa idanunsa jin Malam na cewa. “Waye yayi mata ciki?”. Kusan gaba ɗaya Parlour juyowa sukayi a kaɗe suna kallon Meymey da ta saki wani irin kuka mai cike da shesh-sheƙan kuka. Cikin tsananin tsoro kaɗuwa Yan Hafiz, Yah Yusuf, da Abduraham, kana da iyayensu mata suka zubawa Meymey ido jin abinda take cewa. Shi kuwa Taj dimmmm yaji kunnuwansa sun toshe zuciyarsa ta tsaya da bugawa idanunsa sun daina gani a lokacin da yaji Meymey na cewa. “Yah Afif ne yayi mata c....” By *GARKUWAR MARUBUTA* 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 13* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Page biyu kacal suka rage mu gama free pages bayan wannan, ki biya ki karanta cikin aminci da salama 1k ne kacal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276, kuma mutan Niger 1000fc ne rak zaku biya ta wurin Mommy +22790899076.* Cikin shesh-sheƙan kuka taci gaba da cewa. “Yah Afif ne ya mata ciki babu wanda zai mata ciki a duniya bayan shi,shine ya maidata tamkar matarsa”. Wani irin karkarwa da rawa jikin Yah Abana ya ɗauka maganar tazo masa abaxata baiyi zato ko tsammanin jin irin waɗannan kalaman ba. Rawa zuciyarsa keyi domin sam bata yarda ba kuma bata amince ba lokaci ɗaya yaji jinsa na ƙoƙarin ɗaukewa.. Yayin da Taj kuwa tunaninsa, nazarinsa da ƙwaƙwalwa suka tsaya daga bugawar da suke haka zalika kunnuwansa sunyi dif daga sauraren abinda suke kana idanunsa sunyi dulum daga kallon abinda suke babu abinda yake gani face duhu haka nan yaji numfashinsa na ƙoƙarin barin gangar jikinsa fahimtar yana gab da sumewa In yayi garajene yasan ya ɗan gyara zamansa cikin ƙarfin hali yayi saurin fisgo salati da tasbihi daga cikin zuciyarsa zuwa harshensa duk da bai fito kan lips ɗin sa mutane sunji ba amma da taimakon kalmar _Innalillahi wa'inna ilaihi rajiun Allahumma Ajirni Fii musibati Wa'alhlifli khairan minhaa_ da yake naimaitawa ya bawa numfashinsa damar dai-dai-tuwa ya koma ya zauna kana ya bawa kunnuwansa damar jin maganar da ake yi sai dai har zuwa lokacin zuciyarsa bata samu salama da sa'idar da zata iya komawa bugawanta na aihini ba, sai wani irin bugawa da yake da azabebben ƙarfi da watsa jini liter ɗaya acikin ko wani second saboda ɗinuwar daya shiga... Ummey kam baki ɗaya daskarewa tayi ji take kamar tana yawo asararin samaniya takasa fahimtar cewa araye take ko amace. Mom Amal kuwa wani murmushin jin daɗi tayi tare da cewa. “Uhum haba shiyasa mana ashe da dalili, shiya ko yaushe in akace aje ayi gwaji yake ta lauye-lauye haba koda naji al'amarin nan da ban mamaki da ɗaure kai”. Da sauri Yah Hafiz ya shiga girgiza kansa cikin tsananin mamaki yace. “Noooo!,Noooo dan Allah kuyi shiru bana son jin maganar nan Mom Amal ki daina faɗa”. Yah Yusuf kuwa hannunsa yasa ya toshe kunnuwansa duka biyu yana mai girgiza kansa yayin da Hajiya Halisa Mahaifiyar Yah Hafiz ta juya ta kalli Meymer tare da cewa. “Meymer kiji tsoron Allah kiji tsoron irin abinda kike faɗa Meymey kisan akan wakike magana,Afif fa, Taj kike cewa wai shi yayiwa Laylah ciki ƴar daya ɗauka ya riƙe kana ya maye mata gurbin Uwa, Uba,Yayu da ƴan Uwa yanda yake riƙe da ita yake rainonta tamkar ƴar cikinsa”. Cikin matsanancin kuka Meymey ta rarrafo ta dawo gabanta cikin rawan murya tace. “Wallahi Hajiya idan nayi mishi ƙazafi Ubangiji yana gani, idan na mishi ƙazafi Allah ya hanani kwanciyar hankali. Yanda ya maye mata gurbin uwa, uba haka zalika ya zauna a gurbin mijinta. Kuna gani koda tafiya zaiyi da Laylah yake ya barni baya tafiya dani. ki gafa kwanan nan suka dawo daga Nigeria kwana goma sukayi wallahi ba ƙazafi nake masa ba ai gashi nan suna zaune yayi inkari mana ba gashi nanba, kawai shiru yayi ba tunda yasan baida gsky”. Ta ƙare maganar cikin matsanancin kuka da gigita har kamar numfashinta zai yanke... Ummey kuwa cikin tsananin kaɗuwa jikinta ya ɗibi wani irin karkarwa tamkar wacce aka tsoma cikin ruwan ƙanƙara baki daya ilahirin jikinta ɓari yake numfashinta na kokowa da juna da ƙyar ta samu ta fara fisgo kalmar _Innalillahi wa'inna ilaihi rajiun Allahumma Ajirni Fii musibati Wa'alhlifli khairan Minha_ sune abinda take iya maimaitawa wannan kalmar da take maimaitawa shine yasa Taj ya fara ji da ganin ninsa ya dawowa ahankali ya fara kallon mutanen cikin falon duk da cewa dishi-dishi yake ganinsu. Ganin tana ƙoƙarin shiɗewane yasa cikin sauri Ummu Aryaan ta miƙe kana ta ɗauki roban Swan dake gaban Malam ta balle murfin kana ta tallafe Ummey tasa mata goran abakinta cikin sanyi tace. “Kisha”. Kai Ummey ke girgizawa tare da cewa. “Innalillahi wa'inna ilaihi rajiun”. Ji take sam ba zata iya ba... Yah Yusuf kuwa tun lokacin daya toshe kunnensa yake jujjuya kansa har zuwa yanzu bai bari ba. Yayin da Kabeer da Aryaan kuwa ido suka zubawa malam suna son karantar wani irin yanayi yake ciki da kuma hukuncin da zai iya ɗauka. Malam kuwa baki ɗaya ilahirin jikinsa tsuma yake yayin da idanunsa suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashi kana jijiyoyin kansa sun tashi musamman babban jijiyan dake kan hancinsa ta taso har tana harbawa tsaban tsananin tashin hankali da kiɗima kana da yanda kalmar ta dake shi ji yake cikin gigicewa mai haɗe da ɗimuwa, fahimtar kamar yana gab da ɗimaucewa ne yasa shi maimaita _Allahuma Ajirni Fii musibati Wa'alhlifli khairan Minha Innalillahi wa'inna ilaihi rajiun Lahaula walaƙuwwata illah billah_. Jin yanda sautin addu'oin ke fitowa daga bakinsa ne yasa kowa dake cikin falon ɗaukar addu'oi banda Kabeer, Aryaan da Mom Amal ko wannensu da tunanin da yake aransa. Ita kanta Meymer batasan lokacin data fara maimaita _Innalillahi wa'inna ilaihi rajiun ba_. Laylah kuwa cikin rauni ta saki wani marayan shesh-sheƙan kuka mai haɗe, da ɗimuwa, tashin hankali, gami da rauni ganin yanda baki ɗaya falon ya gigice wasu na kuka wasu sun ɗaura hannuwansu akai zuwa yanzu ta fahimci duk akanta ne sosai kukan da take ya tsananta wanda har ta kai matakin da numfashinta ke shirin barin gangar jikinta. Ganin halin da take cikin yasa Meymer yin saurin rarrafawa ta jawo ta jikinta ta rungumeta tana shafa kanta kana itama tana cigaba da kuka. Cikin shesh-sheƙan kuka tace. “Kiyi haƙuri Laylah ba laifin ki bane ya cuceki ya cuci rayuwarki. Nima ya cuceni ya wulaƙantani iyayena sun aura masani amma bai ɗaukeni matsayin mace ba bai kalleni matsayin mace ba”. Laylah kam kuka take tamkar ranta zai fita Meymer kuwa cikin tashin hankali ta cigaba da cewa. “Baki da laifi dan shine ya cucemu ya wulaƙantar dani ya ajiyeni tamkar gunki bai taɓa kallona Amatsayin matarsa ba ya ɗauke ki ya maye gurbina dake azuciyarsa da kuma jikinsa ya maidake abar biyar buƙatarsa”. Ta kai karshen maganar tana sake fashewa da kuka. Cikin wani irin fusgar magana Malam ya kalli Taj akaro na farko a rayuwarsa yace. “Tajuddeen”. Cikin ruwan murya kana lips ɗin sa na karkarwa ya kira sunansa... Taj kuwa cikin ruɗu ya rarrafo akan gwiwarsa yazo gaban mahaifinsa ya tsugunna. Malam kuwa cikin tsira masa Idanu yace. “Taj me nake ji?,Me ake cewa?,Me zaka iya cewa akai?”. Ina ya kasa mgn sai kansa kawai yake jujjuyawa. Cikin tsananin tsoro da kiɗima Ummey ta dafe hannunta aƙirji tsoronta ya hau-hauwane saboda sanin shi mutum ne da baya taɓa iya kare kansa arayuwarsa, baya taɓa iya in kari kuma, baya musu tafi kowa sanin yanda Taj yake tasan yanda ya tashi ko bashi yayi laifi ba muddin akace shi yayi baya taɓa iya In-kari wannan tunanin da tayi yasa ta saki wani maraitaccen kuka mai cike da ƙuna a zuciya. Taj kuwa kansa kawai yake juyawa. Malam kuwa cikin ɗimuwa da kaɗuwa ya cigaba da cewa. “Taj ka buɗe baki kayi min magana me nake ji?. Me nake ji Tajuddeen?”. A kuma dai-dai lokacin Uncle Jibril tare da Momyn Meymer sukayi sallama jin kamar falon Aruɗe ne yasa cikin sauri suka ƙara sa shiga Falon. Momyn Meymer na shiga cikin sauri ta nufi kan Ummey kana ta tallafo ta jikinta tare da faɗin. “Subhanallah Hajiya Fati meke faruwa?”. Sai kuma tayi saurin juyawa jin Mom Amal na cewa. “Menene ma bai faru ba Hajiya Ruƙayya babu abinda bai faru ba. Tajudden ya zubar mana da mutuncin gida ya tozarmu ya wulaƙantamu ya tozarta tarbiyyar da ake gina wa tun daga kan yayun sa har ƙannensa”. Cikin tsananin mamaki Momyn Meymey ke kallonta tana jin tashin hankali Mom Amal kuwa cikin tarin tsanarsa ta cigaba da cewa. “Tajuddeen ya tozartamu ya bamu kunya yaci amanar hadddar Alkur'ani izu sittin dake kansa Tajuddeen yayi kwance kwance ya ɗibgawa Laylah ciki ya rasa wacce zai yiwa ciki sai marainiya dan jarabar tsiya matarsa bata ishesaba sai ya ƙara da yarinyar amana”. Cikin sauri Ummey ta sake toshe kunnuwanta tare da cewa. “Laaaa, la, laaaa, la No Noooo bana son ji bana son ji. Da sauri Uncle Jabril ya ƙarasa gaban abokinsa ya zauna tare da cewa. “Ya Salam Malam Muhammad kai ya kamata kayi control ɗin su amma sai kuma ka ɗimaucewa ka ɗimautar dasu”. Sai kuma ya juya ya kalli Yah Hafiz yace. “Hafiz ka kwantar da hankalinka”. Sai kuma ya sake maida kallonsa kan Yah Yusuf yace. “Me haka kuke ɗinaucewa!?”. Kallonsa ya kuma mayarwa kan Yah Abdurrahman wanda tunda Meymer tace Afif ne yayiwa Laylah ciki ya buɗe bakinsa bai rufe ba sai hawaye dake ta kwaranyo nasa Aransa yace. kenan mafarkin da nayi yana ƙoƙarin tabbata akwai, ƙalubale da masifa da zata saƙƙo acikin family na, ta watsa mana farin ciki ashe kalubalen dana gaani akan Tajuddeen zai sauƙa!. Yah Abana kuwa hannu ya ɗaga tare da dakatar da Uncle Jibril kana ya kalli Taj da cewa. “Taj me nake ji?,Me Meymey take faɗa?, Tajuddeen me nake ji?,”. Shi kuwa Taj har zuwa lokacin ya kasa magana sai jujjuya kansa yake yayin da lips ɗin sa ke rawa kana Idanunsa sun kada sunyi jawur Araunane ya juya ya kalli Ummey jin tana cewa. “Kayi magana Afif shirunka awannan lokacin zai iya yi mana cutar da har abada baza ku warke ba. Tajuddeen ka buɗe bakinka kayi In-kari akan abinda nake da yaƙinin baza ka aikata shiba”. Araunane ya runtse idanunsa ya kasa magana kwata-kwata bazai iya magana ba dan da zaran ya buɗe baki da niyar zaiyi magana sai yaji tamkar zare ake sawa ana tsuke bakinsa saboda nauyi da zuciyarsa tayi masa. Cikin tsananin fushi Yah Abana ya ɗaga hannu tare da tsinka masa mari akan kumatunsa kana yace. “Ba magana nake maka ba? kayi shiru kana kallona?”. Sake risinar da kansa ƙasa yayi sam ba zai iya magana ba sai dai atake fuskarsa ta rine tayi ja jijiyoyin jikinsa suka tashi lokaci ɗaya jikinsa ya sake rikicewa da karkarwa wani irin kiɗima da ɗimuwa yake ciki wanda tunda yake a iya tsawon rayuwarsa bai taɓa riskar kansa aciki ba, kana nadama mai tarin yawa ta rufe mishi dukkan jiki da zuciya. Hajiya Babba ce ta miƙe kana ta ƙarasa gaban Yah Abana tare da risinawa tace. “Dan Allah na roƙeka dan darajar Annabi kada ka yanke hukunci cikin fushi. ka fini sanin waye Tajuddeen wani ma zai bada shaida akansa, bare kuma kai kada kayi gaggawan yanke hukunci akansa kai masa uzuri sannan ka bashi dama”. Cikin sauri Ummu Aryaan ta taso, ganin abinda take sonyi yasa Aryaan sa hannu da niyyar riketa ahanzarce ta buge hannunsa kana ta tsugunna gefen Yah Abana tare da cewa. “Kada ka manta cewa Tajuddeen bai taɓa kare kansa ba tun yana Karami Tajuddeen bai iya musu ba koba shi ya aikata abuba, kamar yadda ko baya son abu baya musu in ka sashi haka yake aikata shi. Baya iya musu bare ya kare kansa sam bai iya In-kari ba dan Allah dan darajar Annabi ka riƙa maimaita Innalillahi wa'inna ilaihi rajiun za'a samu bakin zaren”. Ummey kam wani irin sassayan kuka take cikin rauni da miƙa lamuranta zuwa ga Ubangiji mabuwayi gagara misali tace. ‘“Taj kayi magana kayi magana”. Baki ɗaya haka falon ya ruɗe ko wannensu na cikin tashin hankali da Alihini saɓanin Aryaan Kabeer Mom Amal... Uncle Jibril kuwa gyaran murya yayi cikin nutsuwa yace. “Kuyi haƙuri kuyi shiru duk abinda yayi tsanani yana tare da sauƙi ”. Jin haka yasa suka shiga maimaita Kalmar Innalillahi wa'inna ilaihi rajiun yayin da muryoyin su keyin ƙasa... Meymer kam rarrafowa gaban Mahaifinta tayi cikin matsanancin kuka tace. “Abba Yah Afif yaci amanata Abba ka aura min Yah Afif na zauna aƙarƙashinsa duk da ba sona yakeyi ba, na bishi nayi mishi biyayya dan nagartasa da ban zaci zai iya aikata wannan ƙazantan ba. Yah Afif ya rasa yarinyar da zai nema yana lalatawa sai yarinyar da ya ajiye agabana na riƙe?, Yarinyar marainiya du-du-du ƴar shekara sha uku”. Cikin wani irin azabebben bugun zuciya Taj ya runtse idanunsa kalaman Meymer na barazanar toshe masa ji cikin matsanancin kuka da sarƙewar murya ta cigaba da cewa. “Yah Afif bai taɓa kallona matsayin matar Aurensa ba, duk tsawon zaman da mukayi dashi watanni kusan takwas kenan yanzu in ƙarya nake mishi gashi nan ya faɗa, wlh ko yatsata bai taɓa riƙewa da sunan muyi zaman aureba ashe duk yana shareni ne dan ya samu Laylah a kusa”. Cikin Mamaki Uncle Jibril ya zuba mata ido ganin tayi shiru ta kife kanta ajikin kujera tana cigaba da kuka. A hankali ya gyara zamansa cikin sanyin murya mai haɗe da tausayin ƴar tasa yace. “Kiyi shiru Mamana kukan nan ya isa haka”. Momy Meymer kuwa cikin wani irin yanayi take kallon Meymer kallo irin na tuhuma da son fahimtar wani abu cikin takaici ta buga mata tsawa tare da cewa. “Dan Allah rufe min baki, kike ta maimaita magana ɗaya kamar kin samu karatun Alkur'ani ko karatun Alqur'ani ba kya maimaita shi haka kamar yanda kike ta maimaita Yah Afif yamin kaza Yah yamin kaza ki rufe min baki ki kuma bace min da gani”. Kallonta Uncle Jibril yau kana yace. “Ya za'a yi ki tayiwa Mamana tsawa? Ki barta bana so kada ki sake yi mata tsawa ki bari taji da abu ɗaya”. Jin abinda ya faɗa yasa tayi Ƙwaffa... Yah Abana kuwa idanunsa sun sake jajur tamkar zasuyi aman wuta kallon Taj yayi kana yace. “Tajudden ka tashi agana kada ka sake zuwa gabana har sai ka tabbatar kana da abinda zaka faɗa min bana son ganinka bana son zargin da ake ya tabbata akan ka. Ka sani in dai zargin da ake ya tabbata akan ka Tajuddeen baka da amfani arayuwata”. Runtse Idanu Ummey tayi kana muryanta na rawa tace. “Innalillahi wa'inna ilaihi rajiun”. Ta ƙare maganar tare da fita ta nufi ɗakinta. Taj kam jikinsa rawa yake so yake ya miƙe yabi bayan Ummey ganin yanda ta fita amma ya kasa. Mikewa Yah Yusuf yayi kana ta tallafe sa ya ɗaga sa kallon yanda jikinsa yake rawa yayi kana ya riƙe sa suka nufi sashen Ummey... A nan cikin falon kuwa Yah Hafiz ne ya juya ya kalli Meymey Muryarsa dashe yace. “Meymey dan Allah dan darajar Annabi kada ki sake faɗan irin wannan kalaman akan Tajuddeen”. Sabon kuka ta fashe dashi kana cikin gaskiyar abinda take gani shine dai-dai tace. “Yah Hafiz abinda ya aikata nake faɗa idan bai aikata ba bazan faɗa ba”. Laylah kam kuka take... Taj da Yah Yusuf kuwa suna shiga Falon Ummey suka sameta zaune gaban 3sitter ta jingina kanta da jiki tana shesh-sheƙan kuka yayin da Zakiyya ke gefenta itama kuka take cikin damuwar ganin halin da Mahaifiyarta ke ciki tace. “Ummey menene ki faɗa min Meyafaru?”. murya can ƙasan maƙoshi sukayi sallama jin sallamarsu yasa ta ɗago kai ganin Taj da Yah Yusuf yasa tayi saurin miƙewa kana ta matsa gabansa muryanta na rawa kana hawaye na zuba daga Idanunta tace. “Ko wani lokaci a kowani yanayi baka iya In-kari kan abinda ya shafe ka baka iya musu adai wannan lokacin muddin baka buɗe baki kayi In-kari ba sannan kayi abinda zai tsarkake kanka daga idon Mahaifinka ba, zaka ja mana baƙin cikin da zamu dawwama aciki Afif ka buɗi baki kayi magana”. Kansa kawai ya girgiza saboda bazai iya ba ya sani haka Allah ya haliccesa Allah yasani bazai iya ba. Kuka Ummey ta fashe dashi mai tsuma zuciya tafi kowa sanin wanene Taj ciki da waje haka zalika tafi kowa sanin Wanene Malam wannan dalili yasa ta sake fashe da kuka. Ganin yanda take kuka yasa Taj zubewa akan gwiwoyinsa ya rasa ya zaiyi kana ya rasa mai zai ce. Cikin sanyi da disashewar murya tace. “In dai baza kayi magana ba, ka cutar dani Tajuddeen adai wannan karon idan har ba kayi magana ba ka gama cutar dani ka cutar da kanka”. Ta ƙare maganar tana zama kan kujera. Yusuf kuwa ganin bazai yi magana ba yasa ya Daga shi suka fita direct mota suka shiga ahankali Yah Yusuf ya kallesa kana yace. “Ina muka nufa?”. Shiru Taj yayi saboda bazai iya magana sai wani irin karkarwa da lips ɗinsa keyi duk da yana taune su maganganun Meymey basu zauna a ransaba ko kaɗan ganin alamun fushi da fusatar Yah Abana ne ya hautsina mishi lissafi. Bayan sun danyi nisa da tafiyar Yah Yusuf ya sake kallo sai tare da cewa. “Afif ina zamuje?,Ko dai in kai ka gidan Addawa ne?”. Kai ya gyada masa kana kai tsaye ya juya akalar Motar zuwa gidan Addawa... A can falon Yah Abana kuwa kallonsu yayi cikin Muryarsa dake ƙunshe da tarin damuwa ya kallesu kana yace. “Ku tashi ku tafi”. Cikin mutuwar jiki kowa ya watse da zullumin dake ransa Momyn Meymer kuwa side ɗin Ummey ta nufa. Meymey kuma hannun Laylah ta riƙe suka fita suna fita tashiga motarta suka wuce gida. Acan gidan Addawa kuma cikin tsananin tashin hankali take sauraren bayanan da Yah Yusuf ke mata baki ɗaya ilahirin jikinta rawa yake kana hawaye na zuba mata tamkar an buɗe famfo tsoronta kuwa sake hau-hawa yake nan take firgici ya bayyana ƙarara asaman fuskarta Babu kalmar da take maimaitawa face Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un tana mai cigaba da cewa. “Ya Allah ka tsare wannan bawan naka da abinda ake zargin sa da aikatawa”. Sosai suka riƙa tausan Taj kan yace wani abu amma ina kasa magana... Jin kiran sallar maghariba ne yasa suka tashi suka tafi masallaci sukayi sallah masallacin unguwar su Addawa ranan agidan Addawa ya kwana anan falonta ita kanta har zuwa lokacin bai buɗi baki ya mata magana ba. Washe gari da Asbah bayan an idar da Sallah yana shiga Falon ya sameta tana waya wanda bisa duk kan alamu da Ummey ce jin tana cewa. “A gidana ya kwana gashi nan kuma tunda yazo bai ce min komai ba haka zalika baiyi magana ba”. Ganin shigowar yasa tayi saurin cewa. “Yawwa gashinan ya dawo yanzu”. Sai kuma ta matsa kusa dashi kana tace. “Tajuddeen ga Ummey ka nan,tana son magana da kai”. Ahankali ya gyaɗa mata kai kana ya zauna tare da karɓan wayar ya manna akunnensa cikin wata iriyar murya mai cike da tsananin sanyi da rauni wanda har ta bawa Ummey tsoro yayi sallama da damuwa atare da ita tace. “Lafiyarka kuwa Tajuddeen?". Cikin sanyayyar murya ya gyada mata kai kamar yana gabanta kana yace. “Lafiya lau Ummey ”. Cikin jin ƙai irin na uwa da ɗanta ɗan ma mafi soyuwa azuciyar ta girgiza kai tare da faɗin. “Tajuddeen Me zaka iya cewa?, Tajuddeen ka buɗe baki kayi magana ”. Idanunsa ya lumshe kana ya taune lips ɗin sa na ƙasa tare da cewa. “Kiyi haƙuri Ummey bazan iya ba”. Wani irin kuka ne yazo mata cikin zubda hawaye tace. “Tajuddeen ba zaka iya bafa kake ce min?. Kasan abinda ake tuhumar ka dashi kuwa?,kasan me ake tuhumar ka dashi Tajuddeen? Kasan cewa duk mutumin daya taɓa Aure mace ko Namiji hukuncin haddi kisa ake yanke masa Tajuddeen shine kake cemin baza ka iya magana ba?”. Kansa ya jinjina yana mai jin tausayinta akasan ransa yace. “Kiyi haƙuri Ummey bazan iya ba kiyi haƙuri, gwara ma a kashenin kawai kowa ma ya huta”. Ya ƙare maganar zucin yana miƙawa Addawa wayar suka ci-gaba da magana. Ganin ya miƙe yasa tayi saurin cewa. “Ina zaka je?”. Ahankali ya motsa laɓɓansa tare da faɗin. “Gida”. Yana fita sai ga Abu Hashim yazo bayan motar ya shiga yana zama wayarsa na ringing yana dubawa yaga Sunan Ishmah na yawo wayar iska mai zafi ya furzar yasan ta kira ne su gaisa kamar yanda suka saba ko wacce safiya kuma yanaji bazai taɓa iya bari bai amsa kiranta ba picking call ɗin yayi ya manna akunnensa ya shiru. Daga ɗaya bangaren cikin sanyayyar murya mai cike da nutsuwa tace. “Barka da Safiya Taj". Ahankali yace. “Hmmm”. Cikin bugawar zuciya mai gauraye da jin alamun yana cikin damuwa tace. “Ya Salam Taj me yake damunka?”. Ahankali ya sake cewa. “Hmmmm”. Still da damuwa afuskarta tace. “Dan Allah Taj na roƙeka kayi min magana in samu salama”. Sai alokacin ya ɗan cije lips ɗin sa murya can ƙasan maƙoshi yace. “Me kika ji”. Tana jujjuya kai tayi saurin cewa. “Taj muryanka ta faɗa min baka cikin nutsuwa da kwanciyar hankali muryanka na tattare da damuwa meke faruwa? Jikina ya jiyo min alamun kana cikin damuwa. Me yasamu Laylah”. Sai alokacin yaji wani irin zafi da zugi azuciyarsa tunaninsa ya tafi kan Laylah dagaske ne kenan?,ciki ne da ita, to idan ya bari aka kashe shi waye zai kula da rayuwar Laylah, Ya Ummeeyshi zataji, waye zai meyewa Ishmah gurbinsa?”. Asanyaye ya furzar da iska mai zafi jin Ishmah na kiransa a hankali yace. “Ba abinda ya samu Laylah Ma'eesha”. Itama cikin sanyi tace. “Toh yanzu meye ne matsalar”. Ahankali ya sake runtse idanunsa tare da faɗin. “Kiyi min Addu'a Ma'eshaa”. Kai ta gyaɗa kana tace. “In sha Allah zanyi, to amman addu'ar me zan maka?”. Tsintar kansa yayi da cewa. “Kiyi min Addu'a Allah ya bani ikon cinye Jarrabawar dake kutso kai cikin rayuwata”. Cikin gamsuwa tace. “In sha Allahu zan yi maka addu'a yanzu ma ina kan sallaya bari nayi maka addu'a”. Kai ya gyada tare da katse kiran. Da kallo tabi wayar jin ya katse yasa ta sake tabbarwa yana cikin matsala. Bisa kan sallaya tayi sujjada tare da cewa. “Ya Allah ka kare wannan bawan naka, ka tsare wannan bawan naka daga sharrin masu sharri, ka ɗaukaka darajarsa ka kare mutuncinsa ka hanasa ta ɓewa ka yalwata duniyarsa da lahirar da farin ciki ka bashi ikon cinye Jarrabawarsa”. Haka dai tayi ta mishi addu'oi... Taj kuwa dai-dai lokacin ya shiga ya samu Meymey na zaune kan 3sitter Laylah na gefenta tana bata tea wani irin kallo ta bishi dashi. Ahankali ya girgiza kansa kana ya saki Murmushi wanda yafi kuka ciwo Murmushin da yake nuna zallan Jarumtakarsa wanda yake nuna rashin nasarar maƙiyansa a kansa Murmushin dake nuni da alamar Fahimtar abinda ke ranta. A hankali ya wuceta ya nufi bedroom ɗinsa yana shiga ya kwanta saboda yanda yake jin tsananin ciwon kai da yanda yake sarawa kwanciya yayi ya rasa mai zai tuna a duniya arayuwar ya rasa abinda zai tuna ranan haka ya yini aɗaki, ko jami'in Sallah agida yake yi tunda ya shiga ɗakin bai fito ba sai washe gari da safe ya fito. Yana fitowa ya tsaya atsakiyar falon kana ya ɗan ɗaga sautin muryan sa da bai fita yace. “Laylah!, Laylah!!, Laylah!!!”. Cikin yanayin tsoro da firgita ta fito da sauri ta tsaya gefensa baki ɗaya ilahirin jikinta na karkarwa matsawa kusa da ita yayi tayi saurin ja da baya Muryarsa asanyaye yace. “Laylah ki tsaya ba abinda zan miki”. Kai ta shiga jujjuya masa amma ba tace komai ba. Yana sauƙe ajiyar zuciya yace. “Yau ba kije school bane?”. Kai ta gyaɗa cikin tarin tsoro tace. “Malam yace in daina zuwa school”. Cikin matsanancin tsoro da firgita ta kai karshen maganar. Da mamaki yace. “Yah Abana da kansa ya faɗi haka?”. Kai ta gyada masa. “To saboda me?”. Ya tambaya yana kallonta murya na rawa tace. “Yace wai kar inje a gane ina da ciki in zubar mishi da darajar sunansa da gidansa”. lip ɗin sa na ƙasa ya cija da ƙarfi tare da juyawa ya fita. Yana fita yayi kiciɓis da motar Amal tana shiga... Yana fita ya wuce asibiti da nufin ko zai iya aiki koda yaje yaji bazai iya aikiba ji yake to mai zai yi daga can ya wuce gidansu Ummey kai tsaye falonta ya wuce yana shiga ya samu falon shiru sai Aunty Maryam da Rashida,Rashida na ganinsa tayi saurin cewa. “Taj". Cikin sanyi ya amsa mata kana ya zauna gefenta itama Aunty Maryam zama tayi gefensa ta zamana sun saka shi a tsakiya. Ummey kuwa jin an kira sunansa ne yasa ta fito daga bedroom bisa duk kan alamu walaha tayi hannunta riƙe da Carbi zama tayi aƙasa agabansa tace. “Afif”. Idanunsa da suka jikkata da dimuwa da tsantsar tashin hankali ya ɗago ya kalleta kana har zuwa lokacin suna nan Ja-ja-jur ahankali tace “Afif na roƙeka ka yakice wannan ɗabi'a taka ka raba bakinka da wannan nauyin, ka cire wannan zurfin cikin, ka kare kanka Tajudden al'amarin nan fa Babba ne kada ka ɗauke shi da wasa lamarine da zai ruguza duk kan wani farin cikinmu”. Ahankali ya juya ya kalli Rashida da tun kiran sunansa bata sake cewa komai ba sai kuka. Aunty Maryam kam zamewa tayi ta kifa kanta jikin kushin ta zubda hawaye. Ahankali ya zame ya zauna gefen Ummey har gwiwoyinsu na gugan juna ahankali ya ɗaga tafukan hannayensa ya daura kan haɓarta ya shiga share mata hawaye. Cikin sanyi tace. “Ba abinda zaka min ka share min hawayena wadda ya wuce ka buɗi baki kayi magana ka fadi abinda yake zahiri ka fadi abinda yake gaskiya, sannan ka fadi abinda yake tsakaninka da Ubangiji ka kuma fadi abinda ka sani akan cikin Laylah”. Runtse idanunsa yayi yana jin tausayinta aƙasan ransa Ummey kam cikin tarin tausayin sa da kuma jin kai ta cigaba da cewa. “Ni ban sani ba Yah Abananka bai sani ba daga kai sai Allah ne kuka sani, dole sai ka buɗi baki kayi mgna ne zamu sani ka samu ka kuɓuta da kan ka Tajuddeen”... Sake runtse idanunsa yayi jin yanda ƙahon zuciyarsa ke harbawa cikin sanyayyan murya yace. “Kiyi haƙuri Ummey bazan iya ba ban san me zanceba”. Cikin sauri da matsanancin tausayinsa Rashida ta ɗago kai tare da cewa. “Afif zurfin cikin ka zai ja mana bala'i kayi magana dole ka fito kayi magana kayi In-kari”. Ahankali ya subkuyar da kansa ƙasa Ummey kam tafin hannunta tasa ta tallafo fuskarsa kana ta riƙe haɓarsa dai-dai gemunsa tace. “Ka kalli Idona ka faɗa min me gaskiyar abinda Meymey ta faɗa”. Cikin yanayin dashi kansa bai sani baya kalleta araunane yace. “Ummey nima ban sani ba”. Idanunta na tsatstsafo da ruwan hawaye tace. “Kamarya baka sani ba?,ka faɗa min gaskiyar abinda Meymey ta faɗa kai kayiwa Laylah ciki?”. Kansa ya sunkuyar tare da cewa. “Ummey i don't know bansan abinda zan ceba”. Yanda yayi maganar ne zai nuna daga ainihin ƙoƙon zuciyarsa yake fita”.... Daga Page 15 zan gama free pages in dai Kinga littafin INDA RAI a wani group ɗin ba group ɗina na littafin ba to na satane kika karanta. By *GARKUWAR MARUBUTA* [1/16, 7:57 AM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 14* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin INDA RAI na kud’ine wannan free pages ne mukeyi kuma suna gab da k’arewa, littafin INDA RAI 1k ne kacal biya ki karanta cikin aminci, zaki iya tura kud’inki ta wannan account d’in 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, zaki tura shaidar biyanki ta wannan numbern- 09097853276. Mutane k’asar Niger kuma 1000fc ne jaka d’aya kenan rak zaku tura kudin karanta littafin +22790899076 ita zaku yiwa magana.* A dai-dai lokacin kuma Addawa tashigo, zama tayi a bayansa kana ta janyo kansa ta manna da guiwowinta, ahankali cikin sanyi da tarin tausayinsa tace. “Kayi gadon zurfin cikin nan, amma kuma a dai wannan karon idan kayi zurfin cikin zai matuk’ar cutar da kai sannan zai cutar damu Afif, ka fito kayi magana ka faɗi abinda ka sani kuma yake shine gaskiya.” Idanunsa da suka sauya launi yayinda jijiyoyin dake cikinsu suka yi jajaye ya ɗago ya kalleta, lips d’insa ya d’an cije kana ahankali yace. “Ba abinda na sani da zan iya cewa”. Da yanayin damuwa Aunty Maryam ta kallesa kana cikin sark’ak’iya tace. “Kamar ya ba abinda ka sani Tajj? wani irin maganane wannan? wacce iriyar magana kake zaka ce mana ba abinda ka sani?” Ta ƙare maganar cike da jin tsoron anya kuwa Taj bai shiga tarkon shaiɗan ba. Dai-dai lokacin Zakiyya ta fito hannunta riƙe da waya tana hawaye wanda bisa alamu da Aunty Halima take waya. Ita kuwa Aunty Halima shesh-sheƙan kuka take Ummey ta mika wa wayar. Ummey na amsa tace. “Toh Halima ya zamuyi addu'a kawai zamuyi masa amma lallai muna cikin ƙalubale, muna gab da fuskantar wani kalubale mafi muni a rayuwarmu, muyi ta addu'a Allah ya kawo mana da sauƙi, ni da Abbanku jiya kwana mukayi ba muyi bacci ba, sannan yau da safe naje na samu Dr. Abbas na duba shi BP d’insa ya hau.” Jin hakan yasa Taj sunkuyar da kansa ƙasa tare da d’an yunƙurawa ya miƙe ahankali. Kallonsa Ummey tayi tare da faɗin. “Ina zakaje?”. Ƙwayar idanunsa ya risinar ƙasa kana atausashe cikin had’iye tarin damuwarsa yace. “Zanje duba Yah Abana”. Ya ida maganar yana mai jin ƙaunar iyayen nasa acikin ransa. Yana shiga ɗakin kuwa ya samu kusan baki daya yayunsa Mazan suna nan sai kuma ya ɗan tsaya jin Yah Hafiz na magana cikin sanyi da taushin lafizi da biyayya yana cewa Mahaifin su. “Abbah kafin ayi komai a nutsu abi abin ban Ahankali, Abba kaine mafi sanin halayen mu gaba ɗayanmu mu ƴaƴanka. Allah ne ya tarbiyyantar damu amma kaine ka daura mu kan hanya Abba ka sani cewa Taj baya ɗaya daga cikin irin mutanen daya kamata ace wannan zargin ya hau kansu, kuma ka tuna cewa Taj mutum ne ajizi dan girman Allah da Manzonsa koda an sameshi da ajizanci a cikin maganar nan ayi mishi uzuri a sassauta mishi”. Cikin sauri Yah Yusuf ya karbi maganar da cewa. “Sosai ma Abba dan Allah asan abinda za'a yi akan maganar nan, ni inaga Maganar nan anyi masa bahagon fahimta ne yarinyar nan Meymey ita kanta batasan mai take faɗa ba”. Ahankali Yah Abana ya ɗago gajiyayyun idanunsa dake nuni da damuwa ya kalli Tajj sai kuma ya sunkuyar da kansa. Tajj kuwa lokaci ɗaya yaji hankalinsa yayi masifar tashi fiye da wanda yake ciki zuwa yanzu ya fahimci mahaifinsa kamar baison ganinsa ne jiki amace ya isa tsakiyarsu kana ya zauna a gaban Yah Abana tare da faɗin. “Yah Abana Barka da safiya”. Batare daya amsa gaisuwar nasa ba yace. “Menene gaskiyar abinda Meymey ta faɗa?” Ahankali ya motsa Lips ɗin sa zuciyarsa na wani irin mummunan bugawa yace. “Ban saniba Yah Abana”. Kai Yah Abana ya kawar batare daya sake bi ta kansa ba. Murya na rawa ya ɗan zuba masa Idanu ganin yanda lokaci ɗaya ya ya faɗa, asanyaye kuma yace. “Yah Abana ya jiki?”. Ƙin amsawa yayi sai ma rufe idanunsa da yayi. Ganin haka yasa ahankali Taj ya zauna kana ya sunkuyar da kansa ƙasa tare da sa hannunsa da nufin kamo ƙafar mahaifin nasa dan yi masa tausa. Saidai hakan baikai ga samuwa ba yayi sauri janye hannunsa sakamakon Yah Abana da ya dakatar dashi ta hanyar janye ƙafarsa. Kafaɗarsa Yah Abdurrahman ya dafa tare da faɗin. “Afif kai namiji ne fa ya kamata ace kana da ƙarfin zuciyar da zaka iya yaƙi da komai. Ya kamata ace zurfin cikin ka ya tsaya iya kan hakuri bakan abinda zai cutar da kai ba kana ya cutar damu”. Sai kuma duk sukayi shiru suna kallon Aryaan dake cewa. “Akan komai dai ɗan Adam zai iya zurfin ciki mun shaida Afif nada zurfin ciki amma dai akan wannan maganar in dai yana da gaskiya yasan ƙazafi akayi masa dole ya fito ya wanke kansa”. Ya ƙare maganar da iya yaƙinin gaskiya yasan dole in dai Afif yana da gaskiya acikin maganar dole ya fito ya wanke kansa. Taj kam shiru yayi batare daya tanka kowa ba... Dai-dai lokacin kuma Meymey ta shigo hannunta riƙe da Laylah da kuma sauran Matan Yah Abana duka su huɗun suna shigowa Hajiya Babba tace. “Ni yanzu ma an tabbatar da cewa shin akwai cikin?,ko yaya?”. Cikin sauƙe nannauyan ajiyar zuciya Yah Hafiz yace. “Batun ciki kam tabbas akwai shi domin likitoci sun gwada an gani cewa akwai ciki harna wata 2”. Cikin sauri Ummu Aryaan tace. “Aje dai asake gwada wa shine kawai abinda yafi dacewa”. Cikin sanyi Meymey dake zaune a gefen Mom Amal tace. “Wani gwaji kuma ya rage Umma? ai ba gwajin daya rage, likitoci nefa sukayi gamayya a kan gwajinta kuma suka tabbatar da cewa tana da ciki.” Kai Ummu Aryaan d’in ta girgiza tare da cewa. “Ai shima Taj ɗin likita ne yaje ya gwada da kansa a tabbatar mana”. Cikin sauri Meymey tace. “Toh Umma in dai da kansa zai gwada ai bazai taɓa fadar gaskiya ba, tunda yasan abinda yake tafiya, nifa nasan cewa shi ya aikata duk wannan abun kuma shima ya sani.” Cikin taɓe baki Aryaan ya karbi maganar ta hanyar cewa. “Toh dama ya za'a yi wanda ake tuhuma ya zama shine mai yin gwaji? kamar fa Shari'a ce ace an bawa mai laifi alƙalanci, kawai Idan ba'a yarda bane sai asake tafiya wani waje aje a gwada”. Cikin sauri Yah Yusuf yace. “Toh shikenan asake ayi wani gwaji a tabbatar”. Asanyaye Yah Abdurrahman yace. “Toh shikenan bari na haɗa ku da abokina Dr Sonail Khan ɗan Indi'a ne amma anan yake aiki ”. Amsawa sukayi saɓanin Tajj da har zuwa lokacin kansa ke k’asa, bayan ciwon da yake ji acikin zuciyarsa ya gaza iya cewa komai, dan har yanzu ganin abun yake kamar acikin mafarki. Meymey, Laylah, Yah Abdurrahman, da kuma Khabeer tare suka tafi asibitin. Bayan awa uku da tafiyarsu suka sake dawowa dai-dai lokacin kuma anyi sallar la'asar bayan sun dawo sun zauna Kabeer da takardun gwajin ke hannunsa ya miƙawa Yah Abana tare da cewa. “Gashi fa tabbas akwai ciki har na tsawon watanni biyu”. Azuciye cikin b’acin rai me tsanani Yah Abana ya wurgawa Tajj takardun, cikin k’unan zuciya ya kuma cewa. “Menene gaskiyar waɗan'nan takardun?Tajuddeen me gaskiyar wannan abin? Me dalilin faruwan haka? Waye Uban cikin nan?”. Ya jero masa duka tsauraran tambayoyin ajere Akuma lokaci ɗaya. Shiru ya kumayi kamar yanda ya saba saboda bazai iya cewa komai ba. Saidai jin ya sake jero mai tambayoyin a hargitse ne ya sashi buɗe baki hankali yace. “Kayi haƙuri ya Abana”. Kusan duk a tare suke kallonsa cike da fara karaya. Ita kuwa Meymey kai ta girgiza alamun. “Toh kun ji dai”. Zazzafan Iska Yah Abana ya furzar daga bakinsa kana akausashe yace. “Tunda baza ka iya magana ba ka fita bana son ganinka!” Ahankali ya yunƙura kana lips ɗinsa na rawa cikin wani irin yanayi me wahalar fassaruwa yace. “Yah Abana kayi haƙuri ka gafarceni”. Idanu Yah Abana ya rumtse tare da nuna masa k’ofa rai b’ace yace. “Ka fita sai lokacin da kasamu hujjoji abakin ka kazo ka faɗa min”. Jikinsa ne gaba d’aya ya d’auki rawa cike da tsananin ruɗani ya miƙe ya nufi hanyar fita. Yana fita kuwa Ummey tabi bayansa da sauri, tare da riƙo hannunsa murya araunace tace. “Ina zaka je Afif?” Kansa dake masifar ciwo ya d’an girgiza kana cikin mawuyacin halin da yake ciki murya can ƙasan maƙoshi yace. “Zan tafi gidan Addawa”. Numfashi ta fesar cikin tsananin tausayin d’an nata tace. “Toh ai itama Addawan tana nan bari in mata magana sai ku tafi tare, kaci abinci ma kuwa?”. Kansa ya girgiza cikin lumshe idanunsa ahankali yace. “Bana jin yunwa". Addawa kuwa jiyo maganar su ne yasa ta fito, tare da bin bayanshi suka shiga mota suka tafi... Ummey kuwa direct parlorn ta ta koma sai kuma ta kalli Rashida dake cewa. “Ummey yayi magana”. Kai ta girgiza tana kokarin maida hawayen dake kokarin zubo mata tace. “Um-um baiyi magana ba Rashida, sai haƙurin da yake badawa dake tayarmin da hankali, Abban ku kuma naga bai fuskanci lamarin nan da fuskar daya kamata a ɗauke shiba yanzu cewa ma yayi baya son ganinsa”. Da sauri Aunty Maryam ta girgiza kanta tana maimaita kalmar “Allahumma Ajirni Fii musibati wa akhlifliy khairan Minha!” Ummey kuwa araunace ta cigaba da cewa. “Yace ya fita ya bashi waje In har ba zai yi magana ba, yayi maganar nan kamar ya manta waye ne Taj kamar ya manta menene halinsa mutumin da tun yana karami baya iya In-kari”. Atsorace Aunty Maryam ke kallonta cikin tarin damuwa kuma tace. “Toh yanzu Ummey ya zamuyi?”. Cikin sanyi Ummey tace. “Yanzu sai dai ku tashi kuje gidan Alaramma Sulaiman tunda ni kona tambayi Abbanku bazai barni in fita ba, kuje kuyi masa bayanin ga abinda yake faruwa inada yakinin shi kaɗai ne zai iya fahimtar da Abbanku wani abu, dan na fahimci Uncle Jibril bazai taba bincike akan duk maganar da Meymey take faɗa ba”. Kai Aunty Maryam suka gyaɗa daga nan suka fita suka tafi kai tsaye gidan Alaramma Sulaiman suka tafi wanda shine Aramman Mahaifinsu mai ja musa baƙi suna tafsir bayan sunje gidan suka masa bayanin iya abinda suka sani. Da kansa ya rakosu har bakin mota yana mai jaddada musu cewa in sha Allahu da daddare zai zo su gana da Yah Abana. Da daddare Alaramma Sulaiman yazo bayan sun zauna da Yah Abana bayanin da Yah Abana ya masa da yanda Taj yaƙi yin magana sai jikinsa yayi sanyi hankalinsa ya tashi Yah Abana kuwa ya ɗaura da cewa. “Kwanan nan fa da Afif yai tafiya Nigeria yarinyar ya ɗauka kwana goma fa sukayi da ita kafin suka dawo, na gaya maka cewa acikin lamuran Taj akwai alamun ayar tambaya?”. Idanunsa ya runtse yana jin wani irin ɗaci acikin azuciyarsa kana ya cigaba da cewa. “Sannan koda nasan tabbas Taj yana da zurfin ciki acikin al'amarin nan kamata yayi ya fito ya wanke kansa asalima Taj sai shiru yake duk abinda na tambayesa sai yace bai sani ba ko yace wai inyi hakuri me haka yake nufi kenan? Taj ya gama ɓata min sunan zuri'a ya gama tozartani ya gama cimin zarafi kana ya ƙasƙantar min da zuri'a”. Cikin sauri sheik Sulaiman yace. “Kada kace haka ka bari sai an tabbatar da komai kayi magana akai ”. Kansa ya girgiza yana mai jin daci azuciyarsa yace. “Wani tabbaci ne ya rage?na rasa ta ina zanbi in samu tabbacin da zan iya gamsuwa dashi”. Haka dai sukayi tattaunawar suka gama bayan Alaramma Sulaiman ya sake tunarsa dashi amma duk da haka basu gano bakin zaren ba... Wasa gaske haka aka ɗauki tsawon kwanaki biyar ana ta gumurzu Taj ya kasa wanke kansa kana Meymey babu abinda take sai ƙara jaddada cewa shi yayiwa Laylah ciki. Ahankali ya shiga cikin gidan yana mai sauke zazzafan Ajiyar zuciya yau kwanansa biyu bai zo gidan ba saboda koda yazo mahaifinsa daga gaisuwarsa da yake amsawa babu wata magana da take sake haɗa su. Ahankali ya ƙarasa shiga Falon Yah Abana zaune ya samu Hajiya Babba agefensa kasancewar yau girkinta ne bayan sun gaisa ne ya ɗan kallesa kana yayi kasa da kansa tare da cewa. “Yah Abana zan ɗan yi tafiya akwai Passenger da zan ɗauka daga nan Ethiopia zuwa Malaysia kwana biyu zanyi.” Ɗagowa yayi ya kallesa cikin tsuke fuska ya kawar da kansa gefe tare da nuna mishi hanyar fita. Jiki amace ya miƙe ya nufi hanyar fita sai kuma ya juya jin Hajiya Babba na cewa. “Allah ya kiyaye hanya Allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya”. “Ameen” Ya amsa kana ya fice, kai tsaye Airport ya nufa ɗakin da za'a masa gwaje-gwaje ya nufa gwajin farko da akayi masa kuwa aka samu jininsa ya hau 180 kana ga tsananin masifar ciwon kai ga kuma zuciyarsa dake harbawa da k’arfi, atak’aice dai matsaloli kusan guda biyar aka samu a tare dashi wanda hakan yasa dole aka soke tashinsa da jirgi wanda dole baza a iya barinsa ya tafi da Passenger ba nan dai aka bashi magunguna kana Driver’n sa ya maida shi gida. Har sun kusa gida ya kalli Abu Hashim tare da cewa. “Ka kaini gidan Addawa”. Kai Abu Hashim ya gyaɗa tare da nufar gidan Addawa. Taj na shiga kiran Ishmah na shigowa wayarsa yana ɗaukar kiran kuwa tace. “Taj”. Murya sanyaye yace. “Na'am”. Cikin tarin damuwa tace. “Kayi min bayani, gaba d’aya ka sauya cikin kwanakin nan guda biyar zuwa bakwai na kasa fahimtar ka, sannan ka kasa yimin bayani, Tajj ya kake son inyi da rayuwata hankalina ya tashi zuciyata ya kasa kwanciya kayi min bayani”. Cikin sanyi ya girgiza kai tare da taune lips ɗin sa cike da b’oye ciwon da yake ji aransa yace. “Ma'eesha ba komai ki cigaba da yimin addu'a kinji ko?”. Kai ta gyaɗa kamar yana agabanta kana murya na rawa tace. “Toh In sha Allah, amma ya jikin Laylah kwana nawa baka haɗani da ita ba”. Iska mai zafi ya furzar daga bakinsa gami da cewa. “In sha Allahu zan haɗaki da ita”. Asanyaye tace. “Toh shikenan”. Washe gari ya kasance ranar Laraba,kamar yanda akasani gidan a cike yake saboda kiran Family meeting da Malam yayi na gaggawa. kamar yanda aka saba gaba ɗaya family’n sa dake state ɗin in dai jumma'a ko ya kira taron gaggawan nan gidan suke zuwa maza da mata. Daidai lokacin da za'a gabatar da Sallah azahar Taj ya tashi daga sahun farko da yake ya kara matsawa gaba sanin cewa muddin yana ƙasar shi yake jansu sallar Juma'a madadin mahaifinsa da kuma kamsutSalawat a masallacin su na gida. Sai kuma ya danyi sauri yaja da baya ganin Yah Abana ya ɗaga masa hannu alamar ya tsaya ahankali ya koma ya tsaya a sahun farko. Yah Abana kuwa da kansa ya tada iƙama akayi sallar azahar, bayan an idar da sallar duk gida suka koma Taj kuwa gidan Addawa ya wuce. Acan gefen gidan Yah Abana kuwa gaba ɗaya yasa Iyalansa suka taru kasancewar Meymey bata zoba yasa Yah Abana ya kalli Kabeer kasancewar shine karami atausace yace. “Kabeer je ka ɗauko min Laylah da Meymey.” Kai Kabeer ya gyaɗa cikin sauri tare da ficewa ya nufi Parking space... Motar Kabeer na ƙoƙarin fita na Taj na shigowa cikin gidan ahankali ya fito daga motar bayan Abu Hashim yayi Parking hannunsa na riƙe da wata sanda me kyau wanda Sheikh Taju Usman Bauchi ya bashi zuwansa Nigeria yana shiga cikin gida direct Falon Ummey sa ya wuce zaune ya sameta tare da Yayunsa har Aunty Halima wacce itama ayau ta taso tazo saboda sun fahimci kiran taron baya rasa nasaba da ɗan uwansu. Ganinta yasa ya fesar da numfashi kana cikin yanayin sanyinsa yace. “Aunty Halima me ya kawo ki Lafiya kuwa?”. Cikin shesh-sheƙan kuka mai cike da tarin tausayinsa tace. “Taju ka manta kenan? Tambayata ma kake lafiya?,ka mance halin da muke ciki?” Adai-dai lokacin kuwa Falon Yah Abana cike yake da ƴaƴansa jikokinsa da kuma Uncle Jibril da Momyn Meymey saura Meymey sannan Laylah, da kuma Khabeer had’i da ahalin Ummey. Cikin hakane Aryaan ya shigo falon Ummey tare da cewa. “Ummey Abba yana neman ku”. Kai ta gyaɗa kana suka miƙe suka bi bayan Aryaan suka shiga dai-dai lokacin kuma motar Kabeer dake dauke da Laylah da Meymey yayi Parking. Yah Abana kuwa hannu ya d’aga tare da nunawa Taj gabansa alamar yaxo ya zauna yayin da baki d’aya sauran ƴaƴansa kowa yana inda yake. Dai-dai lokacin kuma Meymey, Laylah da kuma Kabeer suka shigo falon. Da hannu Yah Abana ya nunawa Meymey da Laylah tsakiyarsu kan su zo su zauna. Suna zama Yah Abana ya ɗago kansa ya kalli Taj tare da cewa. “A yau ɗin nan awannan lokaci nake baka dama ta ƙarshe Akuma yanzu ka buɗe baki kayi min maganar da zan fahimta zan gane. Wannan itace dama ta ƙarshe da zan iya baka a rayuwata ka faɗa min me gaskiyar abinda ke faruwa ya akayi Laylah take da ciki”. Idanunsa da suka kuma yin jawur ya rumtse tare da d’an jijjiga kansa, cikin sanyi had’i da bugawar zuciya ya jujjuya kansa tare da faɗin. “Yah Abana kayi haƙuri ban sani ba….” Jin abunda yace ne kuma yasa baki ɗaya hankalin Ummey, Aunty Rashida, Aunty Maryam, Aunty Halima, da kuma Zakiyya ya tashi sosai, cikin kid’ima had’i da gigituwa suke kallonsa hawaye na zuba a idanunsu. Yah Abana kuwa kallonsa ya mayar kan Meymey dake zaune cikin tsukakkiyar fuska yace. “Meymey me kika ce ranan?” Baki ta bud’e cikin zubda hawayen munafurci tace. “Abbah wallahi Yah Afif shi yayiwa Laylah ciki”. Cikin sauri Hajiya Babba tace. “Toh me hujjarki Sannan menene Shaidar ki?” Cikin shesh-sheƙa ta yi wa Taj da kansa ke ƙasa wani irin kallo kana tace. “Ina da hujjoji da yawa da kuma shaidu”. Lokaci d’aya Yah Abana cikin rashin walwala had’i da tsuke fuska yace. “Menene shaidun ki?” Tana goge hawayen dake zubo mata tace. “A tambayi ita Laylah ɗin”. Da sauri Yah Abana ya juya ya kalli Laylah sai kuma ya maida kallonsa ga Taj. Taj kuwa juyawa yayi yana kallon Laylah haka zalika duk wanda ke cikin Falon Laylah yake kallo. Sabanin Momyn Meymey data zubawa ƴar Tata Idanu tana mai Binta da wani irin kallon tuhuma. Laylah kuwa kanta ta sunkuyar ƙasa. Cikin murya mai cike da damuwa da tsantsar tashin hankali daya bayyana asaman fuska Yah Abana ya kalli Laylah tare da cewa. “Laylah”. Kanta a ƙasa tace. “Na'am”. Sake kiranta yayi amsawa tayi batare data ɗago kanta ba. Cikin sauƙe ajiyar zuciya ya sake kiranta akaro na uku tare da cewa. “Ɗago kanki ki kalleni”. Ahankali ta ɗago kanta ta kallesa. Yana mai jin bugun zuciya yace. “Kinsan akan me ake magana?”. Kai ta gyaɗa. Ɗan muskutawa yayi tare da faɗin. “Magana zakiyi”. Cikin shesh-sheƙan kuka tace. “Eh”. Yana mai runtse idanunsa yace. “Kinsan cewa ance kina da ciki a asibiti?” Jikinta na tawa tana me kokarin danne kukan dake taso mata tace. “Eh”. Cikin sanyi gami da tsoro had’i da fargaba Yah Abana yace. “Laylah waya Miki ciki?”. Kusan baki ɗaya zukatan mutanen dake Falon bugawa yake musamman ma masoyan Taj. More especially Ummey zuciyarta yafi na kowa bugawa. Laylah kuwa cikin sanyi da rawar murya tace. “UNCLE TAJJ NE!!” Lokacin ɗaya Taj yaji baki ɗaya ilahirin jikinsa yana narkewa kamar an shanye jinin jikinsa ji yake tamkar yana zama yashi yana narkewa jin yanda kalmar ya daki ƙoƙon zuciyarsa cikin sauri ya juya ya kalli Laylah sai kuma ya juya ya kalli Meymey da ta saki wani Murmushi wanda daga shi sai Ubangijin daya haliccesa suka san manufarsa. Da sauri Aunty Halima da jikinta ke rawa ta matsa kusa da Laylah’n cikin tarin damuwa da kuma tashin hankali tace. “Laylah kiji tsoron Allah ki faɗi gaskiya Uncle Taj ɗinki nefa”. Kai Laylah ta jinjina cikin zub da hawaye tana me ci gaba da sakin shesh-sheƙan kuka tace. “Wallahi shine kullum in ya dawo gari aɗakina yake kwana kuma yace idan na faɗa zai yankani…” A yanzu kam baki ɗaya ilahirin jikin Taj karkarwa yake da tsuma idanunsa sunyi jajur sun kada tamkar wuta, yayinda yake jin kamar ana kwara masa narkakkiyar dalma tun daga tsakar kansa har zuwa k’asan k’afafunsa, tabbas aduk rayuwarsa bai tab’a ganin tashin hankali da masifa irin wannan ba. Yah Abana kuwa baki daya idanunsa ne suka rikice tare da sauya launi suba farare ba haka kuma su ba jajaye ba, kar-kar-kar haka jikinsa ke rawa. Laylah’n kuwa kuka ta ci gaba da rerawa batare data kuma yin magana ba. Yah Hafiz kuwa cikin wani irin yanayi na tsoro da kiɗima jikinsa na rawa yace. “Meymey kiji tsoron Allah kisan abinda kike faɗa”. Sai alokacin Uncle Jibril ya dago Kai ya kalli Yah Hafiz tare da cewa. “Hafiz Mamana bata ƙarya tun tana ƙarama ban shedeta da ƙarya ba”. Cikin takaici da wani irin yanayi Momyn Meymey ta katsesa da cewa. “Ɗan Adam yana iya sauya hali akowani lokaci Alh ka daina shaidar Meymey”. Cikin sauri Yah Abana ya karɓi maganar da cewa. “Kamar yanda kuma shima Afif dan Adam ne da zai iya sauya halinsa akoda yaushe ba.” Ummey kuwa cikin tashin hankali marar misaltuwa take kallonsa kana murya na rawa cike da tarin d’imuwa had’i da karyewar zuciya tace. “Babana kayi magana! kayi magana Afif ka wanke kanka kace wani abu!!” Me zaice? Bazai iya cewa komai ba, bazai iya ba, kansa juyawa yake yana jin kamar mafarki ne, zuciyarsa tayi masa mugun nauyi, yana jin kamar ana caka masa mashi akan k’ahon zuciyar nasa, komai ya riga da ya k’wace masa, baida wani abunyi sai kansa kawai da yake girgizawa, again ya kasa magana jikinsa ne kawai keta karkarwa. Mom Amal kuwa cikin wata murya me ɗauke da wasu irin manufofi da ita kaɗai tasan ma'anar su tace. “Wannan ma bai isa hujja ba Meymey idan kina da wasu hujjojin sai ki fito dasu mugani ” Cikin sauri Meymey ta ciro wayarta ta bud’e tare da shiga Gallery bayan ta shiga kan abunda take son shiga ta juyo da screen d’in wayar zuwa fuskar Yah Abana. Da sauri Yah Abana ya rumtse idanunsa sai kuma ya miƙe tsaye yayin da numfashinsa ke fusga yana ƙoƙarin ɗauke wa. Sakamakon ganin hoton Taj da yayi tsaye tsirara Laylah na durƙushe ta riƙe gabansa. Da wani irin firgita had’i da gigita mai tsanani ya fara cewa. _“Auzubillahi minarshaiɗanir rajim Auzubillahi da kai Tajudden Subhanallahi da kai Tajuddeen ka ƙazanta ka barranta daga zuri'ata ka barranta daga ahalina.“_ Taj kuwa kansa ya soma girgizawa cikin son yaga abinda Mahaifinsa ya gani da ya kiɗimashi haka. Uncle Jibril kuwa cikin sauri ya miƙe ya karbi wayar daga hannun Meymey yana kallo cikin tashin hankali yace. “Innalillahi wa inna ilaihirraju’un! Afif ka zama guba ka zama ƙazanta acikin al'umma wannan wani irin nasiface Tajudden wace rayuwa ka zaɓawa kan ka”. Ya ƙare maganar tare da sake wayar ta faɗi ƙasa, haka yasa ta ɗan sule zuwa gaban Taj ɗin. Shi kam Taj ya kasa tantance yanayin da yake shin araye yake ne ko ko kuma amace? Saboda ganin tabbas shine a hoton kuma tabbas tsirara yake, kuma tabbas Laylah ce gabansa durƙushe tana riƙe da al'aurarsa, so yake ya rufe ƙwayar idanunsa ya buɗe ko zai daina ganin ɗigon tawadan Allah da yake a saman mararsa wanda yasan duk duniya banda iyayensa da suka raineshi a ƙuruciya babu wanda yasan dashi. Cikin kuka Meymey tace wlh gashi in ba shi bane ya faɗa. Cikin wata iriyar muryar dake cike da hargitsi Yah Abana yace. “Tajjuddeen wai kaine a hoton nan!?”. Cikin jin ƙahon zuciyarsa na gaba da faso ƙirjinsa murya na rawa yace. “Eh Yah Abana ”. Yayi mgnar da iya kar gskyar sanin cewa yess tabbas shi ɗin ne. Ummey kam kuka mai tsanani ta fashe dashi ta kasa magana haka zalika sauran ƴaƴanta da mafi akasarin Mutanen falon... Meymey ko gyara zama tayi tana matsar ƙwalla tace. “Kuma har Video ma akwai”. Cikin sauri Taj ya ɗago kansa jin yanda Yah Abana ya kira sunansa atsawace. Ahankali ya ɗago raunatattun idanunsa da suka ciko da k’walla suna sheƙi ya kallesa jin yana cewa. “Afif ka tashi ka fitar min agidana kabar min gidana bari na har abada bana son ganinka. Bana son sake kallon wannan ƙazantacciyar fuskartaka arayuwata Afif bana son ka sake shigowa cikin gidana. Wallahi Allah kenan idanka sake yarda mu kayi ido huɗu Allah ya isa tsakanina da kai!!!” Cikin tsananin ruɗu mutanen dake falon ke kallonsa. Passs sautin fashewar glass cup dake hannun Yah Abduraham dake bayan Taj ya ratsa kunnuwansu. Shi kuwa Malam cikin tsanar halayyar Taj ya cigaba da cewa. “Kaje na sallamawa duniya kai Afif. Na barrantarwa duniya kai na cireka daga cikin ƴaƴana daga yau ka fita acikin ƴaƴana. Tajudden daga yau Allah ya isa idan har ka sake ambaton sunana a bakin ka matsayin mahaifinka”. Cikin tsananin kaɗuwa mai gauraye da ruɗani Yah Hafiz da Yah Yusuf suka runtse idanunsu suna masu girgiza kansu Yah Abdurrahman kuwa wani sanyayyan kuka ya saki mai cike da ɗimuwa ganin halin tashin hankali da ahalinsa ke ciki. Su Aunty Maryam kuwa, tamkar an daskarar dasu da dusar ƙanƙara haka suka zama. Ummu Aryan ko da Hajia babba riƙe kai sukayi. Mommyn Meymey kuwa da ƙarfi tace. “Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”. Yah Abana kam cikin ƙunan zuciya da tsananin fushi ya cigaba da cewa. “Daga yau ka yanke sunana daga cikin bakinka bana buƙatar ka acikin rayuwata na barrantar da kai daga cikin zuri'ata ku kuma kuji ku shaida dalilin da yasa na taraku”. Sai kuma ya dire maganar yana kallon ƴaƴan nasa. Rai cike da ƙunci ya sauke ajiyar zuciya tare da juyawa falon yana kallon ƴaƴansa yayin da numfashinsa ke sama da ƙasa alamar yana son barin gangar jikinsa yace. “Ku kuma kuji ku shaida duk wanda ya sake mu'amala da Tajudden Allah ya isa ban yafe masa ba, na kuma tsine masa duk wanda ya sake mu'amala dashi bani bashi, ku kuma Matana duk wacce ta kiramin sunan Tajuddeen zata ga fushina, kai kuma Tajuddeen ka tafi kai bazan tsine maka ba, kuma bazan maka baki ba, dan laifin da kayi ya isheka tsinuwa, kawai ni sharaɗin tsinuwana idan ka sake yarda mukayi ido biyu da kai to akan igiyar auren mahaifiyarku kuma bazan yafe maka ba muddin kayi sanadin rabani da Fatima”. Wani irin kuka mai gunji Aunty Halima, Aunty Maryam, Aunty Rashida suka sake suna masu shiga ɗimuwar jin abinda mahaifin nasu ya faɗa. Haka ma sauran Matan Mom Amal kuwa fuskarta ba yabo ba fallasa baza ka gane shin farin ciki take ko akasin saba. Tajudden kuwa kansa na ƙasa ji yake tamkar almara ne ji yake shin mafarki yake ko ko afarke baki daya ƙwaƙwalwarsa da zuciyarsa sun gaza auna kalaman Yah abanansa... Yah Abana kuwa cikin wani irin kunci zuciya mai tafe da nadamar kasancewar Tajudden jininsa ya cigaba da cewa. “Idan ka sake yarda kayi ka nunani a matsayin mahaifinka Allah ya isa ban yafe maka ba idan ka yarda ka sake shigowa gidan nan ko kuma ka sake magana da ɗaya daga cikin Ahalina ban yafe maka ba kuma akan igiyar Auren Mahaifiyar ka... A dai-dai lokacin da yake fadar haka kuma Ummey taja wani dogon numfashi mai nauyi take ta fadi asume. Lokaci ɗaya kukan Aunty Maryam Aunty Halima Aunty Rashida ya sake tsananta Yah Yusuf da Yah Hafiz kuwa da rarrafe suka isa gaban Mahaifinsu kana suka riƙe ƙafafunsa tare da cewa. “Yah Abana kayi haƙuri Tajuddeen bai cancanci wannan abin ba,Wannan hukunci ya masa tsauri kuma muma ya mana tsauri Yah Abana kayi hakuri kada ka yanke wa Tajuddeen hukunci cikin fushi”. Yah Abdurrahman kuwa da ƙarfi ya matso yana buga kafaɗar Tajuddeen tare da cewa. “Afif kayi magana Tajudden ka wanke kanka Tajuddeen ka wanke zargin da Mahaifin mu yake akanka Nasan cewa baka aikata ba”. Taj kam ya kasa motsa laɓɓansa bare ya iya sarrafa harshensa wajen magana. Aryaan da Kabeer kuwa duk da irin tsanarsa da kuma haushinsa da suke ji sai da hukuncin da Yah Abana ya ɗauka ya girgizasu... Cikin sauri Taj ya miƙe jin Yah Abana na cewa. “Ba naso ka ƙara koda 5 minute ne acikin gidana idan ka ƙara ban yafe ba Tajuddeen in ka sake kusanto inda mahaifiyarka take ban yafe ba kuma wallahi akan igiyar Aurenta su Maryam kuma na rabaka dasu”. Ya kai ƙarshen maganar tare da faɗawa kan kushin . Cikin kifewar tunani da cushewar zuciya gami da rashin sanin abinyi Taj ya juya tare da ɗaga ƙafarsa dan fita. Kan glass cup ɗin da ya fashe a hannun Yah Abduraham ya dire ƙafarsa ta hagu. Cikin sauri Ummu Aryan tace. “Ya Salam Taj glass ka taka fa”. Ina baya jinta bare ya iya tsayawa, hasali ma zogin zuciyarsa ya hanasa jin zogin sukan glass ɗin. A haka yaci gaba da takawa yayinda tuni jini yake meye gurbin shatin sawun nashi. Da gudu Aryaan ya shiga ɗakin Yah Abana ya ɗauko maganinsa kana ya basa. Aunty Maryam da Aunty Rashida kuwa Ummey suke jijjigawa. Ganin haka yasa Yah Yusuf cicciɓan Ummey ya nufi asibiti Aunty Maryam da Aunty Rashida na biye dasu. Taj kuwa Ahankali ya ɗan kuma juyowa tare da zaro sandar da Sheikh Tajuh Usman Bauchi ya bashi ya ajiye agaban Mahaifinsa tare da faɗin. “Yah Abana gashi wannan saƙone daga wurin Sheikh Tajuh Usman Bauchi Nigeria daya bani in baka ban samu na baka ba sai yau”. Cikin tsawa Yah Abana yace. “Ka fita daga nan bana son ganinka ka ɓace min da gani idan ka sake minti biyar acikin gidan nan Allah ya isa ban yafe maka ba kuma zan tsine maka!!!” Da sauri ya miƙe tsaye sai kuma ya tsaya jin Yah Abana na cewa. “wannan ɗin kuma da kayiwa ciki kai zaka ɗauketa kasan yanda zakayi da ita,' saboda cikinka ne bana uban kowa ba. Kuma dama kai ka kawota cikin ahlina so yadda ka kwasota ka kawo haka zaka kwahseta ku tafi tare da abin kunyarku. Sannan ka saki Meymey ƴar Aminina ba zata zauna da ƙazamin mazinaci ba ka tabbatar a yau ɗin nan ka saketa”. Idanunsa dake gane masa duhu ya rumtse tare da mik’a hannunsa ya kamo hannun Laylah suka fita. Tafiya kawai yake amma baisan inda yake sa ƙafarsa ba, hasalima baya cikin hayyacin sa, meye zaiyi ko ina zai dosa duk baisani ba, ahaka ya ci gaba da tafiya k’afarsa na zubar da jini sannan yana rik’e da hannun Laylah dake ta kuka haka suka dinga tafiya da sawayen su har suka k’araso gidan Addawa... Cikin murya mafi rauni da sanyi yace. “Addawa ga Laylah nan ance cikine da ita kuma ance wai ni nayi mata cikin kuma itama ta tabbatar da hakan”. Hankali atashe Addawa ta kalli Laylah murya na rawa tace. “Laylah waya miki ciki?”. Da sauri da kuma alamun tsoro Laylah ta matsa gefen Addawa, again murya na rawa tace. “Uncle Taj ne”. Cikin tashin hankali marar misaltuwa Addawa tace. “Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Afif meye gaskiyar maganar? menene gaskiyar lamarin”. Kai ya girgiza kana cikin rauni, had’i da k’unan zuciya me tsanani yace. “Nima ban sani ba Addawa, na dai san Ummey na bata da lafiya sun tafi da ita asibiti Yah Abana yace idan na sake kusantar ta”. Sai kuma yayi shiru yana jin wani abu mai ɗaci na toshe masa maƙoshi. Dai-dai lokacin kuma Aunty Halima tashigo falon da kuka kana ta bawa Addawa labarin abinda ya faru. Hawayen dake zuba a idanunta Addawa ta share mata kana ta kalli Taj tace. “Allah yana tare da mai gaskiya kada ka damu Tajuddeen komai yai farko zaiyi ƙarshe komai yayi tsanani maganinsa Allah”. Idanunsa ya lumshe batare da yace komai ba. Bayan wasu mintunan kuma ya buɗe idanunsa ya kalli Laylah yace. “Laylah ki daina tsorona”. Dan ya lura da yanda yarinyar take tsoronsa abin har mamaki yake bashi. Aranan anan gidan ya yini sai bayan maghariba ya kira Abu Hashim ya kaisa gidansa yana shiga side ɗin sa ya shiga ya tattara duk wasu abubuwa nasa masu muhimmanci da na amfanin yau da kullum ya haɗa. Yana mai jin zamansa a Ethiopia yazo karshe Rayuwa''. a Ethiopia tazo ƙarshe ahankali ya ciri paper guda biyu daga cikin jotter dake cikin Weldrop ɗinsa ya dauki biro ya rubutawa Meymey ta kardan saki sai kuma a ɗayan yayi rubu mai ɗan tsawo kana ya ninke yasa a aljuhu, kana ya cigaba da tattare duk wani abun bukatarsa sannan ya fita. Abu Hashim kuwa ya lura ubangidansa na cikin tashin hankali kai tsaye gidan Addawa suka nufa. Yana shiga gidan Addawa ya samu Aunty Halima da Addawa na zaune sunyi zugum-zugum. Asanyaye yace. “Addawa Ni zan tafi”. Aunty Halima kuwa ganin yana juyawa tace. “Taj ina zaka je?”. Batare da yace mata komai ba ya kalli Addawa tare da cewa. “Ki faɗa mata cewa Yah Abana yace idan wani ahalinsa ya sake yimin magana Allah ya isa bai yafe ba ta kiyaye kada Allah ya isan Mahaifin su ya hau kanta”. Araunane Aunty Halima ta fashe da kuka murya na rawa tace. “Yanzu Taj ina zaka je”. Baice mata komai ba ya juya ya fita ya shiga bayan mota Abu Hashim yaja tare da cewa. “Sir ina zamuje?”. Cikin sanyi murya yace. “Gidan tsohon nan da yasa aka auri ƴarsa……” *Wasa farin girki saidai ba a ma fara wasan ba, kar dai ku manta wannan book d’in na kudine sannan daga page 15 free pages sun k’are saboda haka kar ku bari ayi babu ku, biya 1000 kacal domin samun daman karatu 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa.* *BY* *GARKUWAR MARUBUTA* [1/16, 8:56 PM] Leematu: 📝🕋✈️💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INDA RAI* *BOOK ONE PAGE 15* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Last free page* _LITTAFIN INDA RAI DAI NA KUƊINE 1K NE KACAL, 0661110170 GTBANK Aisha Aliyu Garkuwa. MUTANEN KASAR NIGER KUMA 1000FC JAKA ƊAYA KENAN RAK ZAKU BIYA TA WURIN MOMMY +22790899076_ *Last free page! Last free page!! Last free page!!! Daga wannan Page 15 ɗin na kaɗe na gama free pages koda Kinga littafin INDA RAI a wani group ɗin ki wata ta tura miki to ba satane kuma haƙƙin mallakarsa nawa ne, in kuma baki/baka biyaba kika/ka karantaba mgnar gaskiya haƙƙina dai bazan yafe ba. Littafin INDA RAI na kiɗine ki biya ka biya ku karanta cikin aminci ba haƙƙin kowa bisa kanku a rayuwar nan ta duniya kada ka raina haƙƙin wani dan haka gwara ku biya, 1k ne rak fa 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. Ku kuma mutanen Niger ga number wacce zakuyiwa magana ku biya ta wurinta +22790899076. Dan Allah in dai kin san zaki sayane ki kin sayane dan ki fidda min littafina ki barmin abina ko ki gaya min in maida Miki 1k dinki.* Cikin mamaki Abu Hashim ya ɗan juyo ya kalli ubangida nasa, tare da ɗan rage gudun motar jin yana faɗin. “Gidan su yarinyar nan da mahaifinta keta kuka a aureta zamu je”. Ya ƙare maganar murya can ƙasan maƙoshinsa, tare da rumtse idanunsa saboda suya da ƙunci da zuciyarsa keyi, wanda ya hanashi jin azabar yankar da glass cup ɗin daya fashe a hannun Yah Abduraham. Wani irin sassayan numfashi Abu Hashim ɗin ya fesar zuciyarsa cike da rauni da tsananin tausayin ubangidan nashi, domin yaga tsananin damuwa tare dashi duk da bai fahimci me nene ainihin matsalarsa ba. cikin girmamawa yace. “Sir gidansu Adaya kenan”. Ya dire ayar tambayar yana nazarin halayen Adaya da binciken da yayi a kanta ya nuna mishi. A hankali ya ɗan gyara zamansa tare da kallon Tajj ɗin ta mirror. So yake yayi mishi cikekken bayanin akan tarbiyya da halayyar Adaya to Amman ta ina zai fara? More especially yanzu da yaga ubangidan nashi yana cikin yanayi mai wuyar fahimta, saboda zurfin cikin sa da haƙurinsa da jumriyarsa, yasa bazaka iya tantance halin da yake cikiba. Shi kuwa Taj. Numfashi mai zafi ya fesar dai-dai lokacin da yaga sun ɓullo kan titin nan da bazai taɓa mancewa a rayuwarsa ba. A hankali ya dire ganinsa kan masallacin da ƙaddarar auren Adaya ya riskeshi a ciki. A hankali ya ɗagawa Abu Hashim hannu jin yana faɗin. “Sir lamarin yarinyar fa, ba daɗi a bisa binciken da...”. Sai kuma yayi shiru ganin Taj ɗin ya ɗaga masa hannu tare da jujjuya mishi kai. Shi kuwa Abu Hashim a hankali ya sauƙe numfashi tare da fuskantar gate ɗin gidansu Adaya, kana ya matsa hon. Da sauri maigadin gidan ya leƙo, ganin dantsatsetsiyar motar dake tsaye tana zuba ƙyalli ne yasashi saurin buɗe musu gate ɗin. A hankali ya yayi parking, tare da buɗe marfin motar ya fito yana mgnar zuci. Nazari yau kusan kwana ashirin da biyar kenan da yin wannan binciken Amman ya rasa ta ina zai fara faɗawa ogan nashi sabida ganin tun ranar da aka ɗaura auren bai sakeyi mishi mgnarba, gashi ya roƙeshi mgnar ta kasance sirri a tsakaninsu. Da sauri ya ɗan miƙawa Maigadin hannu tare dayin mishi sallama yana mai mmkin wani irin kallon da maigadin ke binshi dashi. Shi kuwa Maigadin cikin nazari da tuno fuskar Abu Hashim ɗin da dan farin sani gani da yayi mishi a ranar da yace ya aura wa ɗansa Tajuddeen Adaya, cikin tsananin jin daɗi yace. “Mahaifin Tajuddeen mijin da ka aurawa Adaya ko!”. Da sauri Abu Hashim ya gyaɗa mushi kai yana mai mamakin yadda akayi bai mance fuskarsa da sunansa ba harma da sunan Tajuddeen ɗin. “Kai Masha Allah, yau mai gidan zaiji kekkyawan labari da yake fata”. Ya ƙare maganar yana murmushi. Shi kuwa Abu Hashim cikin sanyi yace. “Masha Allah, to kayi mana sallama dashi, kace dashi yau ga mijin Adaya na kawoshi”. Gyara tsayuwarsa yayi tare da ɗan jim kaɗan cikin sanyi jiki yace. “Baya gida, yau kwanansa biyu a asibiti, ciwonsa ya tashi”. Cikin sanyi da alamun damuwa ya ƙare maganar, shi kuwa Abu Hashim cike da tausayawa yace. “Ayyah Allah ya bashi lfy, to Ma'aruf fa?”. Yana ɗan sauƙe numfashi yace. “Duk basa gidan sai Adaya itama yanzu ta dawo, daga asibitin da ƙaninta to shi yanzu ya fita”. Shi kuwa Tajj shiru yayi cikin motar tamkar ba kowa, haka nan yakeji duniyar na juya mishi. Ji yake yi tamkar ba'a raye yake ba, haka nan yakejin ƙasar Ethiopia tamishi zafi da ƙunci, to me zai yi a cikin ƙasar tunda Yah Abana ya barrantar dashi da kowa nashi. Sai kuma ya rumtse idanunsa da ƙarfi saboda wani irin ƙunci da zuciyarsa keyi masa, so yake yayi tunanin ta ina zai fara bawa wannan kamilin dottijon haƙuri akan abinda yasan in yayinshi dottijon zaiji ƙuncin zuciya da rayuwa. Shi kuwa Abu Hashim a hankali yace to. “To ayi mana iso da ita ɗiyar tawa ace mata ga mijin ya iso”. To yace jiki a mace ya nufi cikin gidan domin ya san wacece Adaya da kuma yadda take ƙin batun aure, dama yadda take wargaza duk aurenta da mahaifinta ke shiryawa, da wannan nazarin ya nufi size ɗin Ummin Adayan inda yake jiyo kiɗa na tashi. Bakin motar Abu Hashim ya dawo, tare da ɗan leƙawa ta ciki kaɗan. Ganin haka ne yasa Taj ɗin ɗan sauƙe glass ɗin kaɗan tare da zuba mishi ido. Cikin girmamawa ya gaya mishi yadda sukayi da Mai gadin. Kai kawai ya jinjina mishi. Ita kuwa Adaya da ɗan sauri ta miƙe tsaye daga zaman da take a gaban dressing mirror bisa dukkan alamu yanzu ta fito wanka. Dan Towel ne a daure a ƙirjinta. Jin yadda ake ta buga ƙofar ne, yasa tayi saurin jawo hijabin dake gifenta ta zura shi kana ta nufi ƙofar. Ido ta zuba wa Maigadin nasu lokacin data buɗe ƙofar. Shi kuwa ɗan rusunar da kanshi yayi yana maijin kiɗin data sake yana buwayarsa. “Lfy meke faruwa?”. Tayi tambayar tana girgiza ƙugunta, saboda haka take bata taɓa iya nitsuwa. Ita a zatonta su Ummi ne suka dawo. “Kinyi baƙi ne!”. Ya faɗa yana ɗan jan baya. “Toh kace su iso mana, ya za'ayi ka barsu a waje, su Asina ne da Izzin suka zama baƙi kuma”. Tayi tambayar da alamun tana tsumayin jiransu ne, zasu fita su tafi wurin ibadar rawar da suka ɗaurawa kansu. Cikin sauri yace. “A'a basu bane!”. Tana mai ɗan juya ido tace. “Toh su waye ne?”. Cike da tsoro yace. “Bawan Allah nanne daya aurawa ɗansa ke, to shine yazo da mijin naki”. Wani irin murmushin mai sauti ta saki tare da juyi a tsakiyar Parlour kana tace. “Da gaske?”. Da sauri yace. “Wallahi kuwa gasu can a harabar gidan”. Ya ƙare maganar yana mai kafeta da ido da mamakin yadda fuskantar ta cika da farin ciki. Ita kuwa Adaya cikin Tsananin jin daɗi samun damar yadda zata watsa auren ba tare da wani mushkila ba, kasancewar ba kowa a gidan babu mai taka mata birki da fesa mishi salon tijarar da zatasa dole a yau ɗin a yanzu ya saketa ta samu damar cimma burinta cike da jin daɗi tace. “Alhamdulillah”. Sai kuma tayi maza ta wuce ta gefenshi tare da cewa. “Bari in kawo maka key ɗin BQ kaje ka buɗe mishi kace ya isa”. To yace kana ya bita da ido. Da sauri ta dawo tare da miƙa mushi key ɗin. “Yauwa Baba ya yanayinshi yake?”. Yana ɗan lallonta yace. “Toh gsky dai ban ganshi ba, Amman zan iya nazartan yanayin mahaifin nasa mutumin kirkine, kuma shima ɗan hakanne domin naji Muryar karatun Sheykh Afif Muhammad Taj ne ke tashi a cikin motar tasa bisa alamu mutanene managarta ne masu kamala”. Da sauri tace. “To je kayi mishi iso”. Ta ƙare maganar tana komawa ciki. Wayarta ta ɗauka tare da dannawa Asina kira bugu ɗaya ana biyu ta ɗauka. “Ke wai dan Allah kuna inane har yanzu baku iso ba?”. Cikin juya ido Asina tace. “Gani nan ban fito Bama Izzin nake jira yazo ta ɗaukeni”. Wani dogon tsaki taja tare da cewa. “Kai Izzin na mana wulakanci wlh rashin mota na damunmu, Amman ba komai nasan in sha Allah muna dawowa gasar rawar nan, motoci sai wanda mukeso zamu hau, ke dai muyi fatan Allah ya bamu sa'a”. Cikin ƙwaffa Asina tace. “Wlh kuwa Kinga nayi ta kiranshi ma baya ɗauka.” Tana gyara wuyan hijab dinta tace. “Dan Allah ki fito ki hau taxi ki taho, Kinga wai yanzu wannan wai Tajuddeen da Abpu keta cewa mijina, ne yazo so kuyi sauri kuzo mu tace mishi mutunci dan naji alamun ustadz ne so da makircin karuwaci zamu sa ya sakeni yanzu”. Cikin sauri Asina tace. “Kan bala'i gani nan fitowa yanzu kice zamu goge haddar kan ustadz”. Cikin jin daɗi tace. “Fes ma kuwa. Yauwa maza kiyi sauri bari in kira banzannan kuma, dan kin san dashi abin zaifi tafiya zaifi zargin Izzin ɗin Guy ɗin dake ɗebe min kewa ne Kinga saki dolen doliya kafinma su Ummi su dawo munkorasu”. Da sauri Asina ta miƙe tsaye, tare da katse kiran kana ta fitowa Parlour inda ta samu tsohuwar kakarta wacce tsufa ya cimmata. “Yanzu Asina bazakiyi kanki faɗa ki raba kanki da wannan shegen yaronya ku kama kanku ke da Adaya kusan cewa akwai mutuwa da kwanciyar ƙabari da hisabiba. Tana yamutsa fuska tace. “Ni Kinga tafiyata ki rufe ƙofarki, dan acan zamu kwana, saboda rihazal ya fara zafi”. Taƙare mgnar tana fita, da ido tsohuwar nan ta rakata ido na cikowa da hawaye. Tace. “Yah Allah kaine mai shiryawa ya Rabbi ka shiryi yaran nan shirin musulunci.” Ita kuwa Adaya Parlour ta fito waya na maƙale a kunnenta. Cikin wata iriyar muryar dake nuna Izzin ɗin yana tare da macene yake mata mgn. Tsaki yaja tare da cewa. “Please kayi sauri kazo gidanmu, zamu kora mijin da Abpu ya aura min. Wai yau yazo, karka biya Asina ita ta fito”. Da sauri yace. “Ok gani nan zuwa”. Ya ƙare maganar da raba jikinsa dana arniyar ƙaruwar tasa. A hankali ya iso gefen Abu Hashim tare da cewa. “Bismillah ku isa BQ na buɗe, Adaya nan fitowa”. “To mun gode”. Ya ƙare maganar da bashi hannu. Kai ya gyaɗa kana juya ya koma bakin gate wurin aikinsa wanda yake da ɗan rata daga inda motarsu yake. Da sauri ya buɗewa Taj marfin motar tare da cewa. “Bismillah ka isa”. Cikin sanyi ya ziro ƙafarsa waje tare da fitowa yana mai rumtse idanunsa. A lokacin ɗaya a rana ɗaya ƙaddara ta sauya mishi komai, ta kuma sashi zai akata abubuwan da yafi tsana a rayuwarsa a tun lokacin daya kasance aboki ga Ishmah da ya san sanadin abinda zai aikata yaune ƙaddararta. A hankali yake taka ƙafarsa ya nufi BQ ɗin yana mai jin tausayin Dottijon shin ya zaiyi ya zaiji in yaji abinda zai akaita akan ɗiyarsa to Amman ya zaiyi dole ne ta bar Ethiopia ya kuma nesanta da ita da duk abin cikinta dan gudun tsinuwar mahaifinsa da kuma tsoron kada ya zama silar mutuwar auren iyayensa da gudun faɗawa Allah ya isan mahaifinsa akan ƴan uwansa domin yasan muddin dai in yana cikin Ethiopia to su Aunty Maryam da Rashida dasu Yah Abduraham dasu Hafiz Yusuf bazasu iya hana kansu alaƙa ko magana da shiba. Cikin wannan nazarin ya isa BQ ɗin a hankali ya shiga cikin Parlour mai wadace da tsabta. Sai dai Parlour yana da duhu sosai, kasancewar windows ɗin Parlour a lungu suke kuma a rufe suke ga kuma labuyen dake sassake. Shi yasa haske bai wadaci Parlour ba dan iya ɗan hasken bok ɗin dake wajene ya ɗan bawa Parlour'n haske kaɗan. A hankali ya zauna bisa 1 setter dake fuskantar 3 sitter. Ita kuwa Adaya wani irin makirin murmushi tayi tare da sauƙe Towel ɗin dake ƙirjinta ƙasa ta ɗaurashi bisa ƙugunta, kana ta gyara wuyan hijabinta wanda hakan ya bawa turmusa-turmusan breast ɗin ta dama sakewa da rausaya wa, a haka ta nufi BQ ɗin. A hankali ya Lumshe idanunsa kana ya buɗesu a hankali,. Cikin sanyi ya gyara zamansa saboda ganin duhun ya ɗan raguwa idanunsa kasancewar ya ɗan jima kaɗan a Parlour. Ƙasa yayi da idanunsa lokacin da yaji sallamarta da shigowar ta duk a tare ta haɗasu, Murya cike da kamala yace. “Wa alaikissalam”. Wani irin numfashin da yafi kama da na jarababbun mata ta fesar. Wanda haka yasashi ɗago kansa. Da sauri ya kwaɓe fuska ganin yadda take wani irin girgiza mishi Ballong ɗinta gami da yin wani fitinenne murmushin mai cike da makirci da fidda ainihin rashin jinta da fitsararta. Tare da ware idanunta dan ita har yanzu duhun ya hanata ganin fuskarsa. Shi kuwa Taj. “Wa iyazubullah”. Shine abinda ya furta a kan lips inshi tare da yin ƙasa da kanshi. Jin haka ne yasata saki wani sabon sautin karuwanci fahimtar eh lallai plan dinta zaiyi aiki. A hankali ta matso garesa, tana mai lumshe idanunta tare da shaƙan sassayan ƙamshin jikinsa da yasata saurin rusunawa. Allah ya sani bata taɓa jin ƙamshin wani ɗa namiji da yayi matuƙar sauya mata nutsuwarta ba kamar wannan. Da sauri ya ɗan ƙara matsawa gefen kujerar. Ita kuwa Adaya cikin jin feelings ɗin gsky yana diro mata a jiki da zuciyarta ne, ta dire guiwowinta a ƙasa tare da kife kanta bisa guiwowinshi. “Innalillahi”. Shine abinda kunnenta ya jiyo mata yana faɗi. Shi kuwa Taj wani irin tafasa da ƙuna yaji zuciyarsa tana ruɓanya yi saboda ganin lalacewar da ko a mafarki baya fatan gani. Wani irin zare idanunsa yayi a lokacin da yaji ta sa hannunta duka biyu ta zagayo ƙugunsa murya cike da shu'umci ta fara mgna. “Hi my life, Barka da zuwa”. Hannunshi yasa da sauri ya fara tureta daga jikinsa. Da sauri tasa hannunta ta zare hijabinta tare da cilla shi can gefe. Cikin wani irin tsoron ganin tsananin lalacewar tarbiyyar ta, ya rumtse idanunsa da masifan ƙarfi. Sai kuma yaji jikinsa ya saki wani irin fitinenne rawa da tsuma, lokacin da yaji ta kamo hannunsa ta diresu bisa tamfatsa-tamfatsan breast ɗin ta. Da ƙarfi ya yunƙura da nufin yin mgn sai kuma ya rumtse idanunsa jin ta zira mishi harceta cikin bakinsa. Dai-dai lokacin kuma Ummeey dake kwance bisa gadon asibitin ne takeyin wani irin maraitaccen kuka mai raunata zuciyar mai sauraro. Hannun Malam ɗin dake tsaye a gefentan ta ruƙo cikin tsananin rauni tace. “Dan Allah Malam kada ka nesan tani da Afi...”. Da sauri yasa hannunsa ya rufe mata bakinta fuska cike da fusata gami da tsana da hargitsewar tunani yace. “Kada ki kira min sunansa, wlh muddin kika sake kira min sunansa a bakin aurenki, kuma in har ya zama sanadin rabuwata dake bazan taɓa yafe masa ba, domin ya rabani da mace mafi soyuwa da jinƙai a gareni, duk kuma ɗan dake jinina in ya kira min sunansa ko yayi alaƙa dashi Allah ya isa ban yafe ba, kuma tsinuwata zatabi bayan Allah ya isan”. Da ƙarfu Yah Hafiz, Yusuf, Abduraham, Maryam, Rashida, Zakiya, Halima dama duk sauran suka rumtse idanunsa. Addawa kuwa cikin sanyi ta kalli ɗiyartata cikin bada umarni tace. “Fatima in dai ni na haifeki, kuma zakiyi min biyayya to ban yarda ba ban yafe ba ki sake kira mishi sunan da yace in kin kira akan aurenki ba”. Cikin tsoro da tashin hankali Ummeyn Taj ɗin ta kalli mahaifiyar tata tana mai zubda hawaye masu ƙuna tace. “Innalillahi wa innalillahi rajiun, Allahumma ajjirni fi musibati wa...”. Sai kuma ta kasa ƙarasa saboda numfashi daya toshe mata daga ƙasan zuciyarta domin zafin abubuwan sunyi mata yawa. Ita kuwa Addawa da sauri ta juya ta fice. Cikin sassarfa Rashida tabi bayanta. Shi kuwa Malam cikin zafin zuciya yake mgnar zuci da take iyakar gskyar sace “Wallahi Allah kenan kab cikin Matana babu macen da ɗanta zaiyi abinda Taj ya aikata, ban haɗa da ita na sakaba. Allah kaine mafi sanin irin yadda ka jarabci zuciyata da son Fatima shiyasa ban haɗa da ita na korata da ɗanta ba”. Sai kuma ya juya ya fita. Su Hafiz kuwa zagaye Ummeey sukayi suna bata baki.. Nigeria acan Adamawa kuwa, sosai jihar ke cika tib da baƙin manya malamai da ƙananan saboda ƙaratowar taron ƙarawa juna sani, da haɗa kan izala da ɗarika da za'ayi a jihar. Anyi yarjejeniyar yin taron a Adamawa ne, saboda kab Nijeriya Adamawa ne dai muka rage da tutar Shehu Usmanu danfodiyo, hatta Sokoto da yake tushen Shehu tuni tutarsa daya kafa musu ta ƙare. Sai na Yola Adamawan Modibbo Adama Yola dogge doggitore. To Shi yasa taron ya kasance anan. Tuni Mai girma shugaban izala ta ƙasa yake amsar tawagar bakwancin malaman suna na kasar. Yayinda Masarautar Lamiɗo kuma yake mai masauƙin malam ɗarika da sarakunan gargajiya da suka samu daman halartar. Kasan cewar yau Laraba gobe al'hamis jibi jumma'a da dare ne za'ayi zaman. Ishmah ce kwance bisa gadonta, yayinda ƙanwarta autarsu da Hamisu da Adam ke zaune a tsakiya ɗakin suna hira. Tun bayan rasuwar Dadeey itace ta meye musu gurbinta, kamar dai yadda Daddy ta bar mata watsiyar kula da ƙannenan nata. A hankali Rahma ta ɗan miƙo mata plate ɗin data sa mata kankana tana faɗin. “Adda lfy kuwa”. Tana amsar plate ɗin tace. “Yau fa tun safe neke kiran Taj Amman baya ɗagawa”. Gyara zama Adam yayi tare da cewa. “Wata ƙil yana sararin samaniya ne Adda kin sanshi ba mazauni bane”. Da sauri tace. “Kuma baifa cemin zaiyi tafiya ba”. Sai kuma ta amshi wayar ta da Hamisu ke miƙa mata yana faɗin. “Ga Bappa Kawu na kira”. Amsa tayi tare da yin piking call ɗin. Su kuma hirarsu sukaci gaba da yi. A hankali ta sauke numfashi bayan sun gaisa sai kuma ta ɗan zare ido jin yana cewa. “In sha Allah ranar Friday zan shigo Yola zanzo cikin tawagar Sarki Abubakar. Zanzo da cikar shirina in kin amince dani ko a ranar ma a ɗaura mana aure”. A hankali tace. “Uhmmm”. Sai kuma tayi shiru shi kuwa Bappa Kawu cikin sanyi yaci gaba da kafa gwamnatinsa. A can Parlour Abba kuwa kishingiɗe yake yayinda Yah Abubakar ke gefensa waya yakeyi da Uncle Bello. “Toh ai dama rayuwa ta gaji haka, kuma dole Aysha dai aure zamuyi mata. Domin ko ɗazu da Yamma yaron nan Mukhtar saida yazo min da yayansa da bappansa wan mahaifinsa. Kuma yace ranar jumma'a zasu zo Yola. Kaga dole haka zaka daure kayi aure, in dai anyi sadakan arba'in ɗin marigayi ya.” Cikin sanyi da tarin rauni mai raunata zuciya yace. “Kayya ni kuma wani aure ya rage min Yah Bello, ai aure kam sai yara ita dai Mamana in samu tayi sauren shine burina, sai kuma batun auren Adam, kasan jibin za'a kai kefensa”. Cikin sanyi Uncle Bello yace. “To Abdullahi zaka zauna hakane, ai zama haka bazai yuwuba. Dole kayi aure ko dan Rahma da Hamisu”. Cikin sanyi yace. “Hummm”. Littafin INDA RAI na kiɗine karki karanta in baki biyaba dan Allah 1k ne ga account no in da zaki turo min kuɗinku 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, ku kuma mutane Niger ga number Mommy ita zakuyiwa magana ta gaya muku yadda ta inda zaku tura mata kuɗin 1000fc ne haka ɗaya kenan +22790899076 Ethiopia. Motarsu na fita daga gate ɗin Asina na shiga ta ƙaramar ƙofar, da kallo tabi motar tamkar zata liƙe idanunta akai. Yayinda shi kuma Baba mai gadi bin motar yajeyi da idanun tamkar zai liƙasu a jikin motar, har leƙawa yakeyi gami da karkata kanshi, saboda wai ko zai samu yaga angon Adaya. Amman ina hakan bata samuba saboda Glass ɗin motar tintek ce mai ɗan karen duhu gashi kuma dare ne, duk dama dai akwai wadatar haske Amman daga shi har Asina babu wanda ya iya ganinsa. Ita kuwa Asina cikin mamaki take kallon motar har saida ta ɓacewa ganinsu, kafin shima Maigadin ya iya rufe gate ɗin. Da sauri ta nufi cikin gida, da sallama ta shiga Amman shiru ba motsin kowa, da sauri ta juya ta nufi BQ ɗin tunowa cewa Adaya tace can zata sauƙi baƙon nasu. Abu Hashim kuwa driving yakeyi cike da tsananin mamaki mai haɗe da ɗumuwar ganin yadda ogan nashi ya fito daga BQ ɗin. Ta jikin mirror ya ɗan saci kallonsa. Wani irin rawa da tsuma illahirin jikinsa keyi, yayinda gaba ɗaya jijiyoyin saman goshinsa har na kan idanunsa suka tattaso. Yayinda tsikar jikinsa ke tsaye har yanzu. Kana yasa hannunsa duka biyu ya kama kanshi ya matse da masifan ƙarfi. Dai-dai lokacin kuma ya karya kwanar da zai bar layin. A kuma dai-dai lokacin motar Yah Ma'aruf ta danno kai dan shiga layin Yayinda Ummin Adayan ke baya, saboda yau Mommynshi ce zata kwana da Abpu a hospital. Cike da mamaki Ma'aruf ya zaro idanunsa, ganin Fuskar Abu Hashim ta Glass ɗin fuskar gaban motar. Cikin mamaki yace. “Wannan bawan Allah nanne fa daya aurawa ɗansa Adaya”. Cikin sauri Ummi tace. “Kai haba dai ina yake”. Ta ƙare maganar tana leƙa inda ya nuna mata. Shi kuwa Abu Hashim tuni ya hau kan babban titin ya cilla hancin motarsa ya kama hanyar da zata sadashi da Airport. Cikin sauri Ma'aruf yayi sauri dawo da kanshi kan tuƙin da yake yi tare da cewa. “Inaga fa gida yaje”. Da sauri Ummi tace. “Sosai ma, tunda kaga a layin namu ya fito ai, mu ƙarasa gidan. Nasan ai ya samu Aminu a gida.” Ta ƙare maganar tana gyara zamanta cike da jin daɗi tace. “Alhamdulillah Malam zaiji labari mai daɗi”. Cikin jin daɗi Ma'aruf yace. “Sosai ma kuwa, dan wlh nasan da matsalar Adaya ce ƙarin cutarsa”. A can gida kuwa cikin tsananin tsoro da kaɗuwa Asina ke kallon Adaya dake zaune a ƙasa ta haɗe guiwowinta tare da cusa kanta a ciki tana rusa wani irin maraitaccen kuka dake nuna tana cike da jin raɗaɗi. Da sauri ta durƙusa gabanta sai kuma tayi saurin jawo hijabinta ta rufe mata jinkinta tare da cewa. “Innalillahi Adaya me ya faru”. Cikin kuka murya a raunace tace. “Asina ni nayi da yaudara na jawa kaina ya tureni ya targaɗa min ƙugu ya kum.” Sai kuma ta kasa ƙarisawa saboda yadda takeji wani irin fitinenne zogi da raɗaɗin a muhallinta daya ratsa cikin fitar hayyaci. Dai-dai lokacin kuma Ma'aruf yayi parking da sauri ya fito yana tambayar Baba maigadin. “Baba munyi baƙi ne?”. Da sauri ya matso kusa dashi tare da cewa. “Eh yanzu nan suka fita kun haɗu ko, Wannan mutumin ne daya aurawa ɗansa Adaya yazo ya kawo ango”. Cikin sauri Ummi da yanzu ta fito tare da cewa. “Allah dai yasa ya samu Adaya a gida?”. Yana gyaɗa kai yace. “Eh sun ɗan jima ma, bata fito bama tana BQ ɗin”. Ummi najin haka ta juya ta nufi BQ ɗin. Tana shiga ta zare ido cike da mamaki yadda Adaya ke kuka, bayanta ta zauna bisa kujera. Sai kuma tayi saurin ɗan matsawa tare da ƙara buɗe idanunta ganin rafan sabbin kuɗi kusan ɗauri biyar sai kuma wata takarda daga gefensu... Shi kam Taj gaba ɗaya jikinsa rawa yake da tsuma. Haka nan yake ji tamkar ya tsinewa kanshi da kanshi ji yake dama mutuwa kawai yayi ya huta da wadannan jarrabobin da sukayi mishi rubdugu suka sauya rayuwarsa, kenan shi dai Allah bai sashi cikin masu sa'ar aureba. Ya tabbata kenan rayuwarsa ta shiga garari ko dai Yah Abana ya tsine mishi ne, ya tambayi kanshi cike da zulumi. A haka suka isa Airport. Isarsu da 40 minute jirginsu ya tashi daga Ethiopia zuwa Dubai. A hankali Abu Hashim ya daga kansa yana kallon jirgin tare da sauƙe numfashi mai tafe da hawaye. Maganganun Ubangidan nashi na mishi amsa kuwa a kunnuwansa. “Abu Hashim zan bar ƙasar nan, bari kuma na har abadan. Shi yasa na biya na saki Adaya domin bazan tafi inbarta da igiyar aurena a kantaba. Ga kuma wannan takardar itama ta sakice Ka kaiwa Meymey shi ka damƙashi a hannunta.” Wasu hawaye ne masu masifar zafi suka fara kwaranyo mishi wasu na korar wasu lokacin da yaga jirgin ya ɓacewa ganinsa a. “Sir wacce ƙasar zaka koma, kuma ya batun aikinka?”. Ya tuno tambayoyin da yayiwa Ogan nashi da amsa da ya bashi. “Ban saniba Abu Hashim bansan ina zan samu karɓuwa ba, domin gaba ɗaya duniya ta ƙini”. A hankali ya juya akalar motarsa ya nufi gidan Uncle Jibirin. Kamar yadda ya duba tun kafin ya biyo jirgin Dubai cewa washe gari da yamma akwai jirgin Nigeria zai tashi. Hakanne ma ya sashi biyowa Dubai, kasancewar su Ethiopia saura kusan kwana biyu ne kafin jirgin Nigeria ya tashi. Hakance da yammacin al'hamis jirgin Nigeria ya tashi daga Dubai. Yau jumma'a haji babbar rana, sanin Bappa Kawu da iyayensa suna kan hanyarsu ta zuwa ne, yasa Ishmah shirya musu abinci tare da kimtsa BQ da tunda Taj ya koma tsawon kwana talatin kenan ba'a buɗeshi ba sai yau. Ƙarfe goma dai-dai ta gama komai, Kana ta shiga tayi wanka a hankali ta fito tare da zama bakin gado cikin sanyi ta kalli Rahman dake yiwa Khairat kitso. Cikin sanyi dake nuni da tsananin damuwa ta jawo wayarta tare da kiran Taj ɗin a karo na barkatai. Ajiyan zuciya mai nauyi ta sauƙe jin ya amsa kiran, kawai sai ta saki siririn kuka mai sanyin sauti. A hankali ya lunshe idanunsa dai-dai lokacin da yake zaune a gaban Sheykh Tajuh Usman Bauchi da ya kasance ɗaya daga cikin baƙin da aka karrama aka kuma tarba a cikin masarautar Joɗa. A hankali ya kuma buɗesu murya can ƙasan maƙoshinsa yace. “Wayyo Ma'eesha zuciyata zata fashe”. Ya ƙare maganar a saman lips inshi yadda ko Sheykh dake gefensa bai jishi ba. Da sauri tace. “Innalillahi wa innalillahi rajiun, Taj kana ina? Meke damunka? Meyasa wayarka bata shiga? Addawa tace min ba'asan ina kake ba, Please Taj tell me now ina kake?”. Ta ƙare maganar cikin sassayan shesh-sheƙan siririn kuka. Cikin sanyi murya da ƙara jin ƙarfin guiwa da karsashin ƙudurinsa yace. “Maeeshah yi haƙuri kiyi shiru, ina tahowa gareki yanzu”. Daga nan ya katse kiran. Da sauri tace. “Please Taj tsaya”. Sai kuma tayi saurin kiransa ganin ya katse kiran. Sai dai jin wayar bata shigane yasa ta tallabe habarta cike da damuwa. Shi kuwa Taj ido ya zuba Sheykh Tajuh Usman Bauchi dake jinjina mishi kai alamun ƙarfafa guiwa kana ya miƙa mishi hannu tare dayi musu alamun su tafi. Ƙarfe sha daya dai-dai. Adam ya shigo Parlour tare da kiranta a jere a jere. Da sauri ta fito sanye cikin Nevy blue ɗin Turkey Abaya mai masifar sheƙi da sulɓi tayi rolling kanta da ɗan gyalan. Cikin sauri yace. “Abba yayi baki yace, maza-maza ki bani ruwa in kai musu”. Ya ƙare maganar da nufa dinning area Yana buɗe fridge, ita kuma tray dake kan Dinnin table ɗin ta miƙa mushi. Tare da tayashi kwasar Juice tana faɗin. “Ko dai su Bappa Kawu ne suka iso”. Da sauri yace. “A'a”. Tana ajiye gorunan Faro water data ciro a fridge din tace. “To ko dai Uncle Bello ne ya iso”. Ɗaukan trayn yayi tare ficewa bai bata amsaba a bakin Parlour Abban ya haɗu da Yah Muhammad da Uncle Bello da yanzu ne isowarsa. Amsar tryn Yah Muhammad yayi tare da cewa. “Kaje ka ɗauko Cups kuma idan da Nono ma ka kawo in babu a wurinku kaje wurin Asma'u tana dashi ka amso”. Ya ƙare maganar yana komawa ciki. Shi kuwa Adam yana koma Parlour yace. “Adda wai ki bani Nono in akwai”. Cikin sanyi tace. “Baka gaya min su waye bane”. Cikin sauri yace. “Nifa ban gansu ba Amman dai manyan baƙine dan yadda naji Abba da Yah Abubakar suna musu sannu da zuwa da kuma irin motocin da suka zo”. Ya ƙare maganar yana zaro trayn data cikashi da fruits. Sai kuma ta iso tare da ɗago kwarya nono ta miƙa mishi tray ta daura kan kwaryar kana ya fita. A bakin ƙofar Parlour ya haɗu da Yah Abubakar na cewa. “Maza kawosu koma ka ɗauko Cups da mugs da spoon”. Da sauri yace to. Kana ya koma tare da fara haɗa cups da mugs ɗin da spoon kana ya fita. Ita kam Ishmah jiki a sanyaye ta zauna bisa kujerar Dinnin table ɗin, sai kuma ta fara ɗan lallatsa wayarta tare da kiran Bappa Kawu a zatonsa shine ya iso da Sarkin Gombe shiyasa ake musu wannan hidimar. “Hello Bappa Kawu kun iso ko?”. Sai kuma ta ɗanyi shiru tana jin me yake faɗi. “No bamu isoba, muna sabana, kafin mu iso kuma lokacin salla zai ƙarato so zamu wuce masallacin Lamiɗo Berkinɗo Aliyu Mustapha, sai an sauƙo sallan jumma'a zamu zo”. Jin haka ne yasa ta faɗa tunanin to su waye ne sukazo. Shi yatsaya yana ta mata mgn bata jin shi bare ta bashi amsa. Jin shirunne yasa ya katse kiran. A can Parlour Abba kuwa shiru Parlour yayi baka jin mgnar kowa sai sassayan sautin muryar Tajj. Dake ratsa kunnuwansu da zuƙatansu da sasu daskarewa a zaune a hankali yake motsa lips inshi tare da fito da kalaman dake fitowa daga can ƙasan zuciyarsa. A hankali ya ƙara rarrafawa ya matso gaban Abba tare da zubewa kan guiwowinsa duka biyu. Ido suka zuba mishi baki ɗaya. Murya cike da rauni da gskyar zuciyarsa murya cike da rauni yace. “Abba ina son Ishmah, ina kuma roƙonka da girman Allah da Manzonsa ka bani aurenta Abba na fara son Ishmah tun aranan farko dana fara ɗaura idanuna akanta. Abba ina yiwa Ishmah wata irin sihirtacciyar ƙauna wanda zuciyata bazata iya samun nutsuwa ba tare da ita ba”. Sai kuma ya lumshe idanunsa dake cike tab da da ruwan hawaye wanda yake ji tamkar ana sauƙe masa wani abu mai masifar nauyine azuciyarsa bai damu da duk wanda ke falon ba burinsa ya faɗi abinda ke zuciyarsa cikin wanda yake tsagalgalar rayuwarsa cikin gaskiyar abinda ke zuciyarsa na tsawon shekaru yace. “Abbah na ɗauki tsawon shekaru ina dakon soyayyar Ishmah araina itace mace ta farko dana fara so atarihin rayuwata ban taɓa son wata ɗiya mace irin yanda nake sonta ba itace kaɗai nake kallo a duniya a matsayin matar aurena”. Abba, Yah Muhammad Yah Abubakar kam cikin mamaki suke kallonsa, murmushi dake cike da kunya Yah Abubakar yayi tare da zaro wayarsa. Taj kuwa cikin sanyi da taushin lafizi ya cigaba da cewa. “Abbah nayi alƙawari zan riƙe maka Ishmah da amana. Abba Ishmah itace duniyata, itace farin cikia, itace muradin raina, Abba dan girman Allah ka Aura min Ishmah koda zan samu nutsuwa da salama acikin rayuwata. Dan Allah Abba ka kusanta min Ishmah cikin rayuwata ko zan samu sauƙin raraɗi da azaban zafin da ƙaddara ta haddasa min”. ya ƙare maganar cikin wata raunatacciyar murya... Idanu Yah Rabi'u ɗan Uncle Bello ya zuba masa yana hango tsananin soyayyar Ishmah acikin ƙwayar idanunsa tabbas yayi soyayya yasan kuma menene so duk wani abu da Taj ke faɗa yana fitowa ne daga can ainihin ƙoƙon zuciyarsa zuwa kan harshensa babu wani daɗin baki ko yaudara acikin kalamansa. Tunaninsa ne ya katse jin Taj na cigaba da cewa. “Abbah My life is nothing without Ishmah she's one in Trillion in my Heart Abba ina ƙaunar Ishmah da duka zuciyata wanda ban taɓa yiwa wata ɗiya mace ba kuma babu wacce zan yiwa irinsa har gaban Abadan”. Abba kam lumshe idanunsa yayi yana mai jin wani irin nutsuwa na ratsa magudanan jinin jikinsa tamkar ana sauƙe masa ni'imah lokaci ɗaya kwakwalwar sa ta shiga tariyo masa mafarkan da Daddy tace masa tayi akan Taj da Ishmah tabbas Taj shine zaɓin addu'ar da suka daɗewa suna yiwa Ishmah... Uncle Bello kuwa tsuke fuskarsa yayi tare da yin kici-kici da ita tare da tsare Taj ɗin da wani irin kallon tuhuma. Yah Abubakar kuwa cikin matsanancin farin ciki ya gyara zamansa yana mai cigaba da kallon Taj tamkar ya samu TV tare da ci gaba dayi recording duk kalamansa. Aransa yake jin cewa tabbas karshen matsalar Ishmah akan Aure yazo yanaji Aransa cewa lokacin da ƙanwarsa zata kasance da irin abokin zaman da suke mata fata yazo... Cikin rauni gami da neman alfarma Taj ya kalli Sheikh Taju Bauchi tare da cewa. “Yah Sheikh dan Allah kace wani abu da gaske ina matuƙar kaunar Ishmah fiye da tunanin mai tunani nayi dakon soyayyar Ishmah tsawon shekaru wanda a yau bazan iya ɓoyewa ba itace duniyata i love her more than More”. Sheiky Taju Usman Bauchi kuwa wani irin sanyayyan Murmushi yake yi yana mai tuno wasu shekarun baya da yayi wata ƙuriciya akan uwar gidansa na farko daya mata wani irin soyayya da yake ji zai iya sadaukar mata da komai sai yanzu ya fahimci ashe nashi wasa ne ga wanda yake kallon yanzu da za'a ce ya ɗauki rayuwarsa ya bawa Ishmah TOH tabbas shi mai iya aikata hakan ne... Taj kuwa ganin duk sunyi shiri basu ce komai bane yasa ya maida kallonsa kan Abba da har zuwa lokacin fuskarsa na ɗauke da Amintaccen Murmushi cikin karfafawa kansa gwiwa yace. “Abbah nayi al'ƙawari zan zamewa Ishmah bango majinginar tsayuwarta, nayi al'ƙawari zan hana hawayen baƙin ciki kwaranya daga idanun Ishmah. Abba nayi maka al'ƙawarin zan zamewa Ishmah hasken fitilar da zai haskaka zuciyarta da duniyar ta da farin ciki. Abbah nayi al'ƙawari zan kare Ishmah ga duk wani abin cutarwa. Abbah nayi al'ƙawarin zan bawa Ishmah duk kan farin cikin da duk wata maɗaukakiyar ɗiya mace ke samu agidan mijinta. Abba nayi al'ƙawarin baza ku taba danasanin Aurena da Ishmah ba. Abba nayi al'ƙawarin zansa Ishmah ta soni kafin in tabbatar da ita a matsayin matata”. Ya ƙare mgnar cikin bayyanar matsananciyar soyayyar dake ɗawainiya da zuciyarsa da ruhinsa. Kusan duk a tare suka juyi suka zuwaba Uncle Bello idanu jin yana cewa. “B......! *Last free page daga yau na gama free pages na kab daga wannan Page ɗin ki biya ki karanta 1k ne kacal 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276, mutanen Niger kuma 1000fc ne kacal zaku turawa Mommy +22790899076 Jaka ɗaya kenan.* Littafin INDA RAI na kiɗine karki karanta in baki biyaba dan Allah 1k ne ga account no in da zaki turo min kuɗinku 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, ku kuma mutane Niger ga number Mommy ita zakuyiwa magana ta gaya muku yadda ta inda zaku tura mata kuɗin 1000fc ne haka ɗaya kenan +22790899076 By *GARKUWAR MARUBUTA*********************** ⬇ ************************** **********